*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣1️⃣ Busar kalalo ce ta zagaye baki daya karamin garin mai sunna DOGON DUTSI Wannan busa itace ta fitar da kwai da kwarkwatar wanda ya kwana ya kuma wuni a wannan gari Busar ce ta kada hanjin du wani wanda bai tsamaci zuwan wanda ake yiwa busar nan Babu wanda ya san da zuwan ZAKIN SARAKAI garin na dogon dutsi Kusan hankali Tashe sarkin garin ke kallon wanda ya kawo masa labarin tawagar ZAKIN SARAKAI ke ratso garin nasu Mikewa ya yi tsaye a babar fadarshi ya kalli gabas, da yama, kudu, da arewa , cen ya hangi wasu tarin ciyayin ledoji farare wa'inda a da bai gansu ba sai yanzu Hankali a dan tashe ya ce" Zabga, minana naka gani a ceniya? Ka maza ku dauke duk wani tsinke ko idan Mai garin garinmu ya bar garin nan na gile maku kawunnanku !" Du a rikice aka shiga sake kimtsa fadar, duda batada wanu dati, ama a haka aka ci gaba da gyara duk wani abinda ya dace ace an gyara Nan da nan Fadar ta dauki cika, sarki ya je a gurguje ya cenzo sutura da rawani, ya dawo zuciyarsa cike da zulumin abinda ya kawo ZAKIN SARAKAI garinsa A gigice dawakai suka fara shigowa, lokaci daya kuma aka harba bingida irin ta tokar nan ta yi karra mai karfi gabas da yama, kudu da arewa, sama dau dau dau hakan ya sa wandama bai mike tsaye ba mikewa, dogaran garin suka layu layi layi, masu dawakan nan suka ringa kai hari a dandar kasa sunna danna wani irin algaita sunna hobara har sai da suka tada kura sannan suka koma gefe Wani tafkeken mutun, sanye da shiga irin ta dogarai ama ya yi dinki irin na fitsara, na kirayi dinkinsa da fitsara ne domin rigarsa ta dogarai bakinta saman hannunsa, damatsunnansa a fili suke jibga jibga da su sunna huci.......*HURRRRRR*................. Sai da ya wara kafafuwansa ya dauki algaitar dake hannunsa ya kafa a bakinsa ya yi busar da ta karra hargitsa hanjin sarkinsu , ya daga hannunsa ya dajawa kirjinsa duka ya bude katuwar muryarsa ya ce" GYARA KINTSI!, NA CE GYARA KIMTSI! GA ZAKIN SARAKAI TAFE!" Du wani jinnin sarauta nan take ya gurfana, irin gurfanawar nan ta ajiye gwuiwa a kasa da sada kai, ba gurfanawa irin ta kai hannaye da goshi kasa ba , ko daya, irin ta ba baba girman nan ce Motoci ne suka biyo bayan dawakan har su hudu, suka layi a tsakanin mutanen, sai kuma wasu dawakan a bayansu ya zamto sun sakasu a tsakiya ne Shiru wajen ya dauka, fadar du girmanta irin baban fili na masarautar garin sai da ya nemi yin kadan, a hakanma ana ta hanna na waje shigowa domin cincirodon mutane ne ke ta bibilowa ta ko'ina Dama JIRWAI ya ba Sarkin garin dogon Dutsi kan yana iya karasawa wajen babar motar da aka bude Da dan hanzari ya karaso, sai da ya rage tsayinsa sosai ya jimke hannunsa ya bude bakinsa ya ce" Hawa lafiya , sauka lafiya jinnin sarakai, barka da gannin yau cikin koshin lafiya barka da shigowa garin DOGON DUTSI *OUMOUGHLOUK ITIBEL*, Allah ya sa alkhairinka da ya yabanya a duniya ya tardo ni a yau Adalin sarakai" A kalla ya dauki minti biyar da kawo gaisuwarsa sannan wata kafa, mai dauke da dinki irin na sarakai, yadi ne mai haske Sararin samaniya hakan ya sa sai walwal yake, ya dauki dinki na bakin zare da yelow mai dan kyali, kafarsa cikin takalmi kafa ciki irin na sarauta mai lulube da Ado irin na sarakai, ba'a gannin kafarsa ko daya ba'a gannin kalar fatarsa sai hannunsa da ya fitar mai dauke da kira baba, watau yanada girma hannun da kuma jijiyoyi a tsaitsaye a jikinsa, haka kuma hasken farin hannun ba mai ja bane, aa mai haske ne fassss, ya kai shi saman goshinsa ya hangi ranar garin, rana mai zafi mai kwalar kai , rana mai nadar fata sannan ya idasa mikewa ya fito a matsayinsa gaba daya ba tare da ya bar wani saura na jikinsa a cikin motar ba "Adalin kennan, sarkin Kasata, mai tafe da ikon Allah, mai takama da Ayar Allah, namu gwani bai fito dan ya birge wani ba, namu gwani Allah ne ya nadashi ba mutun ba, NA CE GA OUMOUGHLOUK ITIBEL a gabanku!" Wancen mai darjejiyar muryar ya sake fada yana sake hade hadadiyar fuskarsa ta yadda ya karra rikita zukatan masu saurin sarewa da abin tsoratarwa Sarkin dake gurfane ya dan zubawa idannuwansa da su kadai ake iya ganni a bayane, Alkyabarsa ta rufe komai, ga rumfar da karti hudu ke rikewa sunna tafe idan yana tafia, Cike da iza ya waiga Hagu, da damarsa yana kallon Malaman da suka yi tafiyar da su, uwa uba Sarkin dakin duhu dake sanye da bakaken kaya shi din da kansa bakin jikinsa ba abin dadin kallo bane, uwa uba Sharbebiyar wukar dake hannunsa mai walwalwal din alamun kaifi da kaifafa A nutse, cikin tafiar da Allah ya haliceshi da ita, ba tafia ta wulakanci bace dan shi wane ne, tafia ce da Allah ya nada masa ya bashi a jinninsa, RAWANI ne a kansa ba na siya ko na kwace ba!, RAWANI ne a kansa nadin gado da jama'ar garinsa, RAWANI a kansa wanda ya gagari zamani da gwamnatin zamaninsa, shi din da ake kiransa OUMOUGHLOUK ITIBEL ba shi ya nadawa kansa wannan sunna dake nufin Zakin sarakai ba, SU SARAKAN sunne suka bashi wannan sunna, ba dan su birge shi ba, ba dan fin karfi ba, Magana ce ta cencenta..... Eh lalle shi din *ANNEMOKAL ne mai Adalci da Hatsari!* A daidai wajen da aka tanadar masa da kujera ya ja ya tsaya ya karewa kujerar kallo An kawatata da irin ado nasu dan birge shi duda ya zo a lokacin da basu zaci ganninsa ba, ga kuma rantsatsiyar rana a saman kansu Kansa ya dauke a kan Kujerar, wanda hakan ya saka Dogaransa, Malamansa, Sarkin garin nan, dogaran sarkin garin da du wani wanda ya fahimci Nufinsa ba zai zauna ba kallon kallo da kuma sake gyara yannayi, domin idan bai zauna ba, babu wanda zai zauna, haka kuma babu wanda zai mike daga tsugunon nan Tsoho, mafi kusanci da sarkin garin DOGON DUTSI aka yiwa iso, ya karaso ya duka a gaban sarakan biyu dake tsaye, daya na dan nesa da daya kadan, ana faman fifita masu fifitun da ba ratsa alkyabar jikinsu yake ba bale rawanin fuskarsu Takardar dake hannun Dogari ya warware ya bude Rubutu ne a tausashe , mai isar da sako a hargitse Tanbayoyi ne masu rikita cikin mai laifi kamar haka" Asalamu alaikum wa rahamatullah., Menene dalilin da ya sa mai laifi bai amshi hukuncin kisa kamar yadda ya dace ace ya samu ba?, Ko sakon takardar a yanke masa hukuncin kisa bai isowa masarautar Dogon Dutsi ba?" A rikice Sarkin ya kai dubansa kan Zakin SARAKAI, sannan ya sake mayarwa kan Datijo zuciyarsa na dokawa Datijon kansa zufa ce ta shiga karyo masa a fuskarsa Yaya zai yi? Me zai ce? Maganar da ta saka shi sake sada kansa da budar bakinsa a rikice ya ce" RAINA fansa ne ga doguwa idan har ni Datijo Rabe na zama daya daga cikin WA'INDA suka take dokar Zakin SARAKAI!" Ido Sarkin garin ya sake zuba masa, mamaki da tsoron kar dai Datijo ya fitar da kansa ya saka shi bude baki ya ce" Da doguwa kake Rantsewa Datijo? Doguwa fa? Kar ka sako doguwa a kan laifin da muka aikata baki daya!" Ido Zakin sarakai ya rintse, takaici, mamakin mutanen na kama shi, Doguwa, ace har daga bakin sarki sunnanta da nuna ita din wata ce na yawo a fili a gaban jama'arsa? DOGUWA din nan Aljana ce da suke rantsuwa da sunnanta!, Doguwa din nan aba ce wace suka yarda da ita, Doguwa din nan itace babar damuwarsu da shiga a duhunsu, sai dai basu sani bane, bai zo garinsu ba sai da ya shirya, yau sai ya kona gawon doguwa da hannunsa, idan ya so ya kama da wuta dan Girman Allah! Doguwar Banza doguwar wofi? A kausashe, maganarsa ta farko, tunda aka fara kwaramniyar nan, ya bude bakinsa kai tsaye ya yiwa sarkin magana, sarkin kadai, domin mutanen dake nesa babu wanda ya ji furucinsa, na kusan kuwa a lokacin da ya fara sun dode kunnayensu dan ba maganarsu bace A kausashe ya ce" Kana Musulmi? Dan musulmai, jikan musulmai, ja gaban talakawa kake danne hakin wanda aka cuta, wanda ya tarda matar kanninta ya afka mata, ga laifin Fyade, ga na zina, ga na kisa dan ta kiya ya shaketa har ta mace..........? Lalle idan baka yi wasa ba zan zuba maka petrol a jikin bishiyar doguwarka na kone ku tare AMIRU!" Shiry Sarki ya yi yana yawo da idannuwansa zuciyarsa na bugawa, subahanalah, bai san yaya zai yi ba, dama wannan maganar ce ta taso da Zakin sarakai? Ya Allah yau ina zai saka kansa? Sai da magana ta tardo shi cewa a zartar da hukunci daidai da yadda adini ya zo da shi, aka ringa cewa a kasar nan ai ba'a kashewa dan an kashe, ga koken matarsa a gefe domin danta ne na wani gidan kafin ya aureta, sai ya yanke masa zama gidan yari, nufinsu idan tafiya ta yi tafiya aka manta sai su fitar da shi ya gudu, sai gashi wannan abin ya faru? A nutse ya maida hankalinsa wajen Ustaz AL'AMEEN A yanzu sai ya dan bude muryarsa ta yadda du na kusa kusa zai iya ji ya ce" BISMILLAH Ustaz, menene hukuncin wanda ya kashe bawa ba tare da wani laifi ba? A hukuncin an zo da maganar Zamani ne? Ina nufin zamani irin naku wanda hukunce hukuncen adini suka zamto abin gaba a wajenmu?.....Bismillah" Ustaz AL'AMEEN, baban alkali ne ne na kotun musulunci na kasar ZAKIN SARAKAI A nutse Ustaz AL'AMEEN ya matso ya shiga bayani kamar haka" _"A shari'a kisa ba tare da haƙƙi ba babban laifi ne, ba tare da mun ja da tsayi ba, ina ga ubangijinmu da ya haliccemu ya tsara mana yadda zamuyi rayuwarmu, Allah bai yarda wani ya tauye ɗan uwansa ba, hakan yasa da kanshi ya faɗa cewa *ya haramta zalinci a kanshi* bare kuma bayinsa? Manzon tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi saboda ya kiyaye rayukan al'ummarshi ya yi hani mai kaushi akan ko da wanda zai tsorata ɗan uwansa ne, haramun ne musulmi ya tsorata musulmi da abunda zai iya cutarwa ko da kuwa ciki d'aya suka fito, sannan duk dan a nuna mana haƙƙin ɗan adam aka faɗa a hadisi ingantacce idan mutum zai yi yanka to ya wasa wuƙarshi da kyau, sannan ya kyautata yankanshi, ma'ana ita kanta dabbar ba'a yarda a wahalar da ita ba. Ina ga wanda zai kashe rai? A suratul Baƙara aya ta 178 Allah yana cewa *Ya ku waɗanda kukayi imani an wajabta a kanku yin ƙisasi a cikin kisa, ɗa mai ƴanci da mai ƴanci, bawa da bawa, mace da mace*... Ma'ana idan ɗane komai gatanshi idan ya kashe ɗa to shima a kasheshi, idan bawa ne shima ko bawan wanene a kasheshi, a yanzu kuma da ya zamana akwai ƙarancin bayi, dole ne muyi ƙisasi ga duka al'ummarmu, dan duk al'ummar da za ta yi shiru bayan an kashe mata rai, to da yiwuwar iftila'i ya saukar mata, dan kuma a suratul Ma'ida aya ta 32 lokacin da Ƴaƴan Annabi Adam Ƙabila ya kashe Habila Allah yace *Saboda wannan muka wajabta akan ƴaƴan bani isra'ila wanda duk ya kashe wata rai ba tare da wata rai ba (ma'ana idan shima ba kisa ya aikata ba) ko kuma ba tare da fasadi ya aikata a ban ƙasa ba, to fa tamkar ya kashe duka mutanen duniya ne gabaɗaya*...kenan da wannan ina ga zamu iya yankewa wannan hukuncin kisa dan kuwa bayan laifin kisa dake kanshi akwai laifin fasadi aban ƙasa, ba wai tausayi bane kuka nuna mishi da kuka ajeshi, dan Allah ma a aya 93 dake cikin suratul nisa'i cewa yayi *duk wanda ya kashe wani dagangan to makomarsa jahanama ce yana mai dawwama a cikinta kuma Allah yana fushi dashi sannan ya tsine masa albarka kuma ya masa alƙawarin azaba mai girma*."_ Gyara tsayuwarsa yayi tare da ƙara jan alkyabbarsa irin ta malamai fara ƙar sannan yace" Hukuncin kisa ne a kanshi ta hanyar jefewa, ba kuma mu ne muka faɗa ba wannan hukunci shari'a ce ta zo dashi, daga cikin mutane ukun da aka hallata jininsu akwai tsoho mazinaci, ba wai tsoho tukuf ba ake nufi, ana nufin wanda ya taɓa aure ko kuma mai auren, dan a nan soyayyar da zamu nunawa wannan mutum ita ce mu jefeshi da duwatsu har sai ya mutu." Wani irin kuka Matar sarki ta fashe da shi, wanda ta kasa rikewa har sai da hankalin jama'a ya karkata kanta Da sauri aka riketa ana bata baki kan ta yi shiru za'a saurara masa ta bari a gama magana, an tabata mijinta zai nemawa dan rikonsa sauki a wajen Zakin sarakai! A dake ya shiga ratsowa duban jama'ar nan, ya zamto an sake budawa masu biye da shi da rumfarsa suna nemi biyo shi, sai dai lokaci daya ya dakata ya masu nuni da kar su biyo shi, hakan ya sa du wani mai makami wanda ke tafe cikin tawagarsa mikar da makaminsa da kuma shiryawa koda ta kwana Sai da ya zo tsakiya ya tsaya A nutse ya ringa duban jama'ar dake zagaye , har sai da wajen ya sake daukan wani shirun sosai , a tausashe ya bude bakinsa ya ce" Su wanene mu? Me muka taka? Me muke takama da shi? " Ya ajiye maganar yana sake duban du wanni wanda ke iya yin ruwa da tsaki a lamarin Idannuwansa ne basu da sauki a motsinsa, sunne kadai zasu iya nuna maka idan ka tarbi gabansa yana iya cinye namanka danye a masifa, shi yasa ba kowa ke iya ido cikin ido da shi ba, sai wanda ya taki tasa takakiyar shima A kausashe ya dora da fadin" Laifinsa ne bai isa a zartar da hukuncin da ya dace a kansa ba, ko gatansa ne ya haramta masa daukan hukunci?" "Mace ce mai daraja, tana dauke da auren kanninsa a kanta, ya shiga dakinta ya haure mata ta hanyar fyade, shedun bayi bakwai muka samu da tsoro ya hanna su magana!, Ya afka mata, ya yi zina da ita, ihun kukan da take yi ya saka shi shake wuyanta da hannayensa idannuwansa sun rufe burinsa ya kai ga ci!, A haka ya kasheta, da Aurenta, da darajarta , shima da nasa auren, ama dan yana dan gata ne za'a boye laifinsa? Dan yana dan gata za'a kasa zartar masa da hukunci? A gobe idan wani ya aikata wani laifin ana iya tura min takarda dan jiran hukuncin da ya dace dan rashin adalci?" Ya karashe wannan karron da dan karfi, domin sai da Dogari ya bude bakinsa da karfi yana fadin" ALLAH ya huci zuciyarka Zakin sarakai, Allah ya huci zuciyarka" Yan yatsunsa yake ta aukin dannawa da babar yatsarsa dan ya sasauta fushinsa Sai da ya gamsu zai iya magana ya ce" HUKUNCIN dake kanda, bisa koyarwar Addinin Musulunci shine hukuncin kisa!, Bisa hanya mafi wahalarsa ko Allah zai gafarta masa!, Zai fuskanci horo na kwana uku kafin a jefe shi, WANNAN shine hukuncinsa bisa Adalci!" A yanzu kam kukanta kasa rikuwa ya yi, harta ita kanta ta kasa rike kanta, da karfi ta kubce har tana neman yadda alkyabarta da ta daka a yanzu yanzu da zata fito itama. Da gudu ta ringa ratso mutane, lokaci daya mijinta ya hangota haka kuma ya ga sarkin dakin duhu ya ciro sharbebiyar wukarsa ya daga kafa shima ya nufo filin da take kokarin shigowa Bai taba sannin shekarunsa ba zasu hanna shi sauri dan tare iyalinsa ba, sai da ya ga yana kokarin yin sufa ya durfafeta lokaci daya ya damki hannunta ya fincikota baya ya zubar da ita kasa sannan ya kai kasan shima ya yi anfani da damarsa biyu , ta farko ya riketa dan hannata mikewa, ta biyu kansa a kasa ya ce" ALLAH ya huci zuciyar Mai gida, zuciya ce irin ta Uwa ta dibi sarauniyar Dogon dutsi, In ba wannan ba minana a hukuncin nan? Ai maganar Allah aka bida a kulun ita aka yi, Allah ya huci zuciyarka" (Ai maganar Allah ake bi a kulun) Uwar gidan sarkin yake kallo da kukanta da ya cika wajen A nutse ya juya wajen Mahaifiyar yarinyar da aka kashe, wace ta fita hayacinta, ta fige, ta lalace, fuskarta du ta jeme, damuwa ta sakata ta zama wata iri Kai ya cira ya shiga takawa cikin takunsa na kasaita bai ce da dayansu ufan ba har ya karasa wajen Mota zai shiga an bude ana ta yi masa addu'a ya dakata kasa kasa ya furta Dogari magana kamar haka" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣2️⃣ Kai ya cira ya shiga takawa cikin takunsa na kasaita, ba tare da ya cewa dayan su ufan ba har ya karasa wajen motar da aka bude tuni ana ta kirari irin nasa wanda ake binsa da shi da Adu'ar gamawa da duniya da mulki lafiya Ja ya yi ya tsaya ya karra juyowa wajen daukacin jama'ar garin Dogon Dutsi yanai masu kallo irin wanda shi kadai ya san tarin bege, da kaunarsu dake zuciyarsa, ba dan komai ba sai dan kasancewar su yan kasarsa, sannan musulmi, duk da a wannan gari an ribanci jama'a da dama an saka su a harkar bautama wannin ALLAH, ama sai yake jin ciwonsu a cen kasan zuciyarsa harma da son sake tsayawa da jagoran garinsu ko za'a dace a kan abinda yake son fara gabatarwa? Shi din yaro ne a cikin jerin sarakunan KASATA NIJAR, sai dai kuma shine ZAKIN SARAKAN kasata NIJAR kasa kasa ya dubi dogarin ya ce" Idan na je da garaje, na kone baban wajen taronsu dan karra yardarsu wa doguwa, wace itama halitarta wanda ya halici samai da kasai ya yi....me zai faru?" Kansa a kasa yake, yana matukar tatauna abubuwan dake bakinsa, Cheik na gefensa shima da nashi a bakinsa ama bai fada ba domin ba'a bashi damar yin maganar ba A nutse ya ce" Kana da damar yin hakan Allah ya taimakeka, kana da damar konnewa dukan wani lungu da sako babu wanda zai maka fito na fito sai dai ya bi ta kasan kasa ko wanene!, Umarninka muke jira mu zartar ANNEMOKAL ITIBAL!" Ya karashe yana rage tsayinsa sosai kansa a sade Kallon Dogarin nasa yake yi, na hannun damarsa, Sai kuma ya yi dan murmushin da shi kadai ya san ya yi, ya dubi CHEIK a tausashe ya ce" KA FADA MIN GASKIYA CHEIK da abinda fiyayen halita ya yi, ka kwatanta min yadda zan yi koyi....domin na san ba isata ta kawoni inda nake a yanzu ba!" CHEIK ya sauke ajiyar zuciya, domin dama zuciyarsa cike da tsoron kar dai a bada damar yake, dan ya yarda dari bisa dari cewa ba haka bane zai samar da zaman lafiya a kasar nan baki daya ba, daukan makami ba shi bane zaman lafiya, idan aka dauka aka tafi ya tabata wani sai ya shiga an kone abinda ya yarda da shi tare, dan ya samu cetonsa, subahanalah, idan hakan ya faru kuwa zai zamto ne an fara daukan makamai ana yakar junna...... A hankali ya gyara tsayuwarsa ya fuskanci UMUGHLUK ya ce" Shi tsafi gaskiyar mai shi ne, haka kuma sihiri akoy shi mugwayen sihiri kuwa,.........." Ya sake matsowa sosai ya tausasa muryarsa sosai ya ce" Allah ya karra maka lafiya, kaine ke nuna mana kafin mu dauki takobi mu fara anfani da kalaman bakinmu....., Yaki da makami bashida anfani idan har hakan zai zamto yaka na yaka ne, UMUGHLUK zamu fara yin duba da hanyar da aka fara bi aka yaki mutanenmu? Kar mu manta a wasu garuruwan adini ya yi girma da yabanya, a wasun ana yi ne Alhamdulilah a duniya baki daya, yawancin filanin garin nan da aka ribanta a jeji suke zaune, sannin adinin musuluncin sama sama ne, bautar a hasashe ne, ana rayuwa ne da dabobi ana kiwatawa , wasu dabobin ma basu da su sunna rayuwa a wahalce...., Da bare gurbi suka shigo cikinmu sai suka shigo da dabara da wayo irin nasu....., Wani mutumen kauyen saboda magi sai ya rakaka wajen bautarka, wajen bautar da za'a tarar da kade kade dai da sauransu ..... wa'inda mun sani babu abinda yake da saurin yin tasiri a wajen dan Adam irinsu, domin shedan na ciki tsamo tsamo, bale kudade da cima mai kyau, asibitoci da ja a jiki, uwa uba da nunawa nasu abin bautar shi ne na alkhairi shi ne ya dace a bautawa, shi ne mai jin kai, gashi Har ya turo a talafe su? To fa da yawa a haka suka kauce hanya suka fada halaka, da yawa a haka suka kauce hanya, daidaiku ne Allah ya tseratar......." Ya ajiye yana sake kallon yannayin Saraki Ya dora da fadin" Dukan Hanyar da za'a bi dan a nuna masu wanene Ubangijinsu ba zata kai ta laluma da nasiha da wa'azi da ja a jiki ba....., Idan an kone masu a yanzu za'a kona zukatansu, idan har an kone masu a yanzu za'a tunzurasu ne, kuma ba'a isa a hanna su zuwa wani wajen su aikata wanda ya gimami wannan ba, ta yiwu masu halayar garin su bazu wani garin su ja ra'ayin masu jiran su ji amsa irin haka, Ba wai ina nuni cewa nasiha da kawo ayoyin Allah ne zai tseratar da dukannunsu ba, aa, wanin ko me ka nuna masa ya rigaya ya yi nisa...., Mu dai dama kwatantawa ne namu da yaki da abinda Allah ya halata mana mudin ranmu, idan a cikin dari ashirin suka gane mun ci riba ITIFAL..............................., Da so Samu na yi Ya ITIFAL mu bude masu magangannun da suka zo a cikin Alkur'ani, domin kuwa a cikin kaso d'aya na ukun Alƙur'ani ana magana ne akan tauhidi ma'ana kaɗaita Allah, sannan ayoyi bila'adadi Allah ya yi magana akan shirka, idan muka duba Suratul Lukman aya ta 12 inda mahaifi yake wa dansa wasiyya cewa " و إذ قال لقمان لابنه و هو يعظه يبني لا تشرك بالله، إن الشرك لظلم عظيم." "Mahallin sha'ir anan ranka shi daɗe shine shirka, munin shirkar yasa uban ya fara nusar da danshi da lamarinta har ya kirata da zalinci ne mai girma." Suratul Muhammad aya ta 32 tana tunasar damu cewa "Ya ku wad'anda sukayi imani ku yi da'a ga kuyi da'a ga manzonsa, sannan kada ku b'ata ayyukanku. A rayuwar dan adam babu abinda yake saurin ruguza aikinshi kamar shirka, zaka shekara dubu kana aikin lada, amma sakan d'aya ya wadatar ya bata duka wannan ayyukan indai shirka ce ka yi." Kara sadda kanshi yayi ya d'ora da" Akwai bukatar mu fara sanar dasu me ye shirka da illarta, dan daga cikinsu akwai wadda basu san muninta ba, kuma magana ce daga bakin fiyayyen halitta a hadisin Abu Huraira ruwayar Bukhari da Muslim cewa " *Lallai Allah yana kishi, sai dai kishin Allah shine ya ga bawansa na aikata abinda ya haramta masa*, a wani hadisin kuma yana magana ce cewa *Allah na matukar kishin ganin bawansa ya had'a shi da waninsa.*, ranka shi dade, shirkar nan tsabar muninta mai aikata ta ma Allah alkawarin wuta ya masa, kamar a Suratul Fathi aya ta 5 da ya ce *Zai azabtar da munafiki da munafika, na biyu sai ya ce da mushriki da mushrika, bayan shirka ne sannan aka kawo zina sannan Allah ya ce yana hushi kuma ya tsine musu albarka tare da alkwarin wutar masira.* , a suratul bayinat aya ta 5 ma Allah yace *Lallai wadannan kafiran daga ahlil kitabi da kuma mushrikai suna cikin wutar jahanna zasu dawwama a cikinta...*, sarkina, a ganina in dai girman matsalar ya kai haka, to dole sai da laluma za mu bisu da dabara har mu samu cimma nasara, dan bai kamata mu bari lamarin ya kai kamar yadda muka shina *a suratul Suratu Baqara aya ta 101 wanda suka tabbatar mana da lallai mai hada bautar Allah da wani to tabbas kafiri ne*." Sosai ya sake zuba masu ido, a hankali ya sauke ajiyar zuciya bai ce komai ba ya shige bayan motar ya zauna yana gyara zamansa irin zaman daram din nan ya sake waigowa ya zubawa jama'ar ido har suka tatara da jama'arsa suka fice gaba dayansu dafifin yara da manya na daga masu hannu ana masu byby da rakiyar motocinsu da dawakansu A hankali a hankali masarautar ta ringa hautsinewa, labarin barinsa garin ya idasa rikita garin Dogon dutsi, bama kamar dangin matar sarki da ita din kanta A rikice ta karasa dakinta ta dauki wayarta ta shiga kiran number auntynta, watau mata a wajen sarkin garin TANUT Hajia na dagawa ta shiga labarta mata abinda yake faruwa tana sheka kuka Itama hankalinta ya yi kololuwar tashi, domin a yaune ta ji ainahin maganar ta gaskiya, a da an sanar mata cewa matar ce ta tardo shi da lalata garin ya guje mata tsautsayi ya sauka a kanta har ta rasa numfashinta Rai bace, hankali tashe ta ce" Dama kin san abinda ya faru kennan kika yi sanyar da har UMUGHLUK ya san labarin? Yaya kika yarda uwar yarinyar ta fito ta zaga gari har ta fito magana ta fito duniya ya ji? Ke kin san baya tare da zalunci kuma ja tsoron uban wani yake yi ba, kina tunanin shi kawun nasa ya isa ya tankwasashi ne a kan gaskiyarsa? Bari ki ji, muma a nan a cikin tamu muke, domin magana ce boyayiya ke son fitowa saman ruwa amkar an zuba mai saman ruwa, maganar dake sirrin dakansa ce ke son fitowa fili, wace in tsoron da abinda Sarkin garina zai fanshi zaman lafiyarsa!, Ba zan ce maki babu maganar gannin Uban yara ba, ama ban maki alkawarin komai a kai ba, kar ki manta har yanzu Mahfuz bai gama kason da aka dibar masa ba, da ya isa da wani abin da ya hanna hakan!, Ki san hanyar da zaki fitar da danki idan ba zaki iya jure a kashe maki shi ba, ko ki san hanyar da zaki maye gawarsa da ta wani! Wannan shine shawarata a gareki , nima ta kaina nake!" Murya a raunane ta ce" Yanzu kina tunanin idan na masa hanya ya gudu ba zai gano nice na aikata haka ba? Idan ya gano kin san halinsa fa komai yana iya yanke min ba kunyar wani zai ji ba" Lebenta ta dantse da karfi tana jin ciwon lamarin yaron Tunani ta yi mai dan tsayi kadan , sannan ta ce" Zamu fara karkatawa wajen neman sulhu kan kar a kashe shi a barshi a suluru har wa'adinsa ya cika......, Ki sani mulkin UMUGHLUK ITIFAL takaitace ne! Idan lokacin hakan ya kai sai mu ci karanmu babu babaka!" Dakatar da shashekar kukanta ta yi a hankali ta ce" Kamar yaya takaitace ne?" Idannuwa Gimbiyar Tanut ta dago da dan sauri, sai kuma ta batar da maganar ta hanyar mikewa tana fadin" Ki share hawayenki zan kirayeki, ki fara neman mafita, nima zan buga ta nan, ga Bahija cen bata da lafiya ne zan tabo ki" Tsai ta yi da wayar a hannunta ta zubawa waje daya ido, ta tabata abinda ya kai bakin Gimbiya da yin wannan furuci abu ne ginane mai tushe, ta tabata Gimbiya ba zata yarda bakinta ya furta furucin da yake na karya ba, abinda ta fi ja ta tsaya a lamarin daya ne tak..... Shin menene boyeyen digadigin abinda aka boye a lamarin Zakin sarakai?, Basaraken da ya gaji sarauta ne aka yiwa furucin takaitaciyar sarauta ke gabansa yaro mai jinni a jika?, Shin tanada labarin wani abu zai sameshi ta sanadin mijinta ko kuma wata boyayiya take kasa a kan usulinsa? .....wannan furuci ya sakata manta abinda ya dace ace ta mike ta kamanta a matsayinta na uwa, watau taya yaronta rokon gafarar ubangijinsa da fatan hakan shine alkhairi a gareshi Sai ta bige da dogaro da maganar cewa yaronta zai fito ya rayu cikin isa da iza ya ci gaba da wulakantar da ƴaƴan mutane dan yanada DAMA!, Karshema zaman jiran kiran Hajiarta ta yi dan ta bata dama ta gama da sangartaciyar y'arta mai raini da raina na gaba da ita! __________________________________ A TANUT Da dan sauri Gimbiya ta karasa Tankamemen falon y'arta tana fadin" Fadime? Fadime? Shin bata yarda ta sha maganin bane?" FADIME mace ta hannun damarta, wace ke tare da ita tun shekarun tuwo, take bauta mata da ƴaƴanta ta juyo tana sauke ajiyar zuciya da sake rage tsayinta ta ce" Allah ya karra maki lafiya, tace ba zata sha maganin ba, shine nake jira idan ta farka ko zata yarda ta amsa?" Takalmin dake kafarta mai laushi ta cire ta haye saman gadon tana dora kafarta daya ta tankwashe ta saka hannayenta biyu ta yaye abin rufar ta miko hannunta da tsawa tsawa ta ce" Dan Allah bani ni, tun dazu na baki wannan dan aikin ki wani zo ki sakata a gaba bayan kin san dan kankin kanta ba sha zata yi ba? Tafi dan Allah ke kam kwata kwata bakida wani anfani a rayuwa sai shirme!" Jikinta na dan rawa ta rage tsayinta sosai ta mika mata kofin dake dauke da maganin sannan ta nemi afuwarta ta juya har tamkar zata kifa dan sauri Ina jira na ga an dago wata yar yarinya a bata abin nan, sai gani na yi an talafo wata gindimemiyar budurwa ana ta faman shafa gefe da gefen fuskarta ana tambayarta idan har jikinta ne ya yi kamari a kirayi docter? Ita kuwa tana langwabewa da ture maganin wanda kana ganni zaka fahimci tsabar tabara ce irin ta wanda ya samu dama ke damun wannan baiwar Allah mai sunna BAHIJA ya a wajen sarkin garin TANUT, wato ya mace daya kwal a wajen uwar gidansa sarautar mata ........................................................... Saurin da Fadime take bata zame a ko'ina ba sai a wajen ciyayin dake cen bangaren dawakai A hankali ta ringa amsa gaisuwar da bayin dake kasanta ke yi mata cikin girmamawa a matsayinta na baiwa mafi kusanci da uwar gidan sarki kuma mata a wajen sarkin dogarai wanda yake sshine sarkin dogarai kuma shine wanda ke kula da lamarin dawakan wajen Tunda ta karaso yake kallonta da ciyawar dake jibge a hannunsa wadda ya kwaso dan ya ciyar da bakin doki, domin dokin ne yakeda fada babu mai rabarsa da garaje Dakatawa ya yi sosai yana kallonta har ta karaso A hankali ta dan dago idannuwanta da suka shanye tamkar wace ta shanye su da gangan , bayan haka suke, da farko an zatama ciwon ido me da ita, domin idannuwanta a shanye suke koda yaushe irin tana kallon kasan idon nan, kuma girmansu da tudun samansu ya daka idan ta lumshe din kamar mai barci, ba kasafai take maka kallon cikin ido ba dan akan ce da ita wai kallonta na kayar da gaba, ta dan dago ta yi masa kallo a fuzge sannan ta maida dubanta wajen dokin dake kakawar da kai irin jibgegen dokin nan Murmushi ta yi har kananun hakoranta duka bayana jere reras ta daga hannunta fari kallll tana kallonsa ta ce" Zan so na shafa Dokin nan" Dokin ya kalla, sai kuma ya dake kallonta Shekarun matarsa sun ja, shi din kansa ya fi a irga yana neman hutu ko dan yarsa kwalin kwal da Allah ya bashi a duniya dan su koma inda take so su rayu su kula da ita, ama abin ya gagara, yarinyar ta ki yarda ta zauna a masarautar zai je ya daukota ya kawota ama tana gannin mijin kanwar maman nata zai koma kauyen *LABA* zata silale ta gudu, tamkar wace ake cizo a masarautar, a rayuwarta ita dama lamarin rayuwar sarauta ce sam ba tata ba, bata so bata kauna, ita tana kaunar rayuwa ce irin ta yanci, yadda zata bararaje ta walwala abinta, shi yasa take guduwa tana barinsu su kadai hankalinta kwonce Dokin ya sake kallo, sai ya yi murmushi ya kade hannayensa yana girgiza kansa ya shiga nufar bangarensu yana fadin" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣3️⃣ Dokin ya sake kallo ya yi murmushi, sai ya kade hannayensa ya shiga nufar bangarensu yana fadin" So kike yi a garin Tanut a gile min kaina? Domin wannan dokin mahaukacin doki ne, idan ya bale nima a tsorace nake, kina so ya bige ki na soke shi? Bayan zuciyar sarkin garin nan ne?......... Fadime ni kam ina mamakin me saraki ya gani a dokin nan da ya kamu da kaunarsa, doki bakin kirin ba annuri ko daya? Gashin idannuwansama bakake ne sidik" Dan murmushi ta yi tana tafe jikinta tamkar bata da lakka, hakan ya dakashi fakatawa yans dubanta sosai ya ce" INNARTA?, kamar hankalinki a tashe yake?" Dakatawar ta yi itama da tafiar da take yi ta juyo tana kallonsa A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta karasa wajen zama ta zauna fuskarta na nuna alhinun da zuciyarta ke ciki Jiki ba karfi ya karasa yana sakin labulen kofarsu ya zauna a gefenta kadan yana kallonta da yaren buzanci ya ce" Yauma wani abin ya faru da ke da uwar gijiyarki ne?" Idannuwan nata ta dake dagowa tana kallonsa Numfashi ta ja mai zafi, kai itafa a yanzu bama wannan ne damuwarta ba, danma rai da riko ne ta kasa sabawa da wulakancin dake bilowa lokaci zuwa lokaci a tsakaninta da Gimbiya, lalle a karkashinta take, ama an jima da goge bauta irin ta zamanin bayi, albashi garesu, aiki suke yi, dandai aiki ne na mudin rai, ama an jima da goge irin rayuwar nan ta rashin yanci, shi yasa take shan wahala, shi yasa ta kasa yin rayuwaa irin ta daba, shi yasa take yawan jin wani abu a cen kasan zuciyarta idan aka wulakantata Dan murmushi ta yi tana kallonsa ta ce" ABANTA, ka san da ta kai shekara goma sha tara har ta dora a duniya? Nakan damu da tarin zulumin tarbiyarta, ka san wacece kanwata ka san halayanta, duda na san ba zata taba bari ta zamto mai irin halayar nan ba, ama ina cike da tsoron ta zamto wata iri daban, ina matukar son na ajiye aikina na koma kusa da yarinyata, da ace a zaman kalau ne ka dan da yanzu tana dakinta, irin halayarta na rashin zama waje daya kan dagan hankali, kar aje tana cen tana cafta tarai a dajin Allah, kar aje abubuwan da take gwadawa na jarumtar da ya dace ace namiji ke nuna su ta damka ta mayar ruwan darenta, kana tune dawowa ka yi ka tarar ta yanka sanuwar Ladan dan ta tungujeni, ........ni kam damuwar yarinyata ta fara taba min nutsuwata, idan har zan iya ci gaba da wannan aiki to fa sai idan na mikata dakin mijinta" Ajiyar zuciy ya sauke ya gyara zamansa yana sake fuskantarta Murmushi ya yi yana kada kai, ba dan komai ba sai dan tino damarar yarinyar tasa, Rawani take yi tamkar dan saurayi tana shagalinta hankali kwonce Dira take ta haye saman doki ta warci linzaminsa ta kada akalarsa tun bata wuce sha uku ba Hm........... Lalle ya san ya dace ya nemi zama wa matarsa koda shi bai zauna ba, domin gidan Hindu ba gidan rainin budurwa bane, to wane ba wanema a cikinsu daga ita har mijinta? Ai tamkar makaho ne a saman makahon doki........... Da son kwontar mata da hankali ya sake fuskantarta, hannayenta masu laushi da hasken fari dan tsaftarta da kuma zama a cikin ACn da take koda taushe a bangaren Gimbiya ya dan karra murzawa a hankali ya ce" In sha Allah, zan kamanta sake shigar da takardar ajiyewar aikinki, idan amsa ta fito mana sai mu je mu daukota, ama nima ba zan so ku fita nesa da ni ba, domin ina da bukatarku a gefena kin ji INNARTA?" kai ta gyada tana sauke dan murmushi, duda tana cike da tunanin kamar aikin banza ne, domin an taba shugar da takardar a gabanta uwar gijiyarta ta yaga takardar tana fadin shirmen banza ba zata ajiye aiki yanzu ba, ama a yanzun tana tunanin ko a dace, domin ta kula ta ishi Gimbiya, bata san itama har ga Allah ta fara gajiyawa ba, zata so ta samu yanci irin na kowa ta kula da y'arta da kuma mijinta, ba bauta a banza ba! ___________________________________ Shigar yamaci suka yiwa baban garin na AGADAZ bayan tafia ta kwana biyu a hanya sanadiyar nisan dake tsakanin ziyarar da ya kai garin Dogon dutsi da kuma dan tsayawar da suka yi a hanya dan yada zango a wata masarautar da ziyara irin ta zumunci Tunda suka shigo baban garin ya haye saman bijimin dokinsa fari kal mai dauke da kwaliya irin ta ALBE da azurfa harda salkar zinari Kamar yadda yake da haske a fatar jikinsa, haka suturar jikinsa take, da kuma kamanin DOKINSA, takalmin kafarsa kafa ciki ne shima sai nasa walwalin yake Jama'ar gari du an fito tarbansa, tamkar wanda ya yi doguwar tafia Yawanci masoya ne, wasun kuwa yan su ga ya dawo da ransa da lafiyarsa ne? Taro dai taro na alkhairi ne, domin babu yaro babu baba, babu talaka ko mai kudi, sunna girmamashi sunna kaunarsa A hankali ya ringa tafiyar da dokinsa ga dogarai a gefe da gefe rike da lema tafkekiya itama sai walwali take ta haske ko'ina Kafafuwan dokin kan bada sauti cas cas idan ya ajiye kofaton kafarsa dalilin kwaliyar dake jikin kafar A haka har suka karasa baban masalacin masarautar suka yada zango dan gabatar da sallar Magariba da kuma ta isha'i Sai da suka gama sallar sannan ya shige Fada a nutse ya nufi bangarensa direct domin a mugun gajiye yake, danma an saba da hawa da saukar da kuma doguwar tafiyar? Ga umarah da zai tafi wace zai yi tafiyar sirri domin baya so a san inda ya nufa A nutse ya kama hannun falonsa bayan sun gama gaisawa da UMMA, wace take jalabiyarsa uwar goyonsa shi da kanwarsa sama sama domin ba zai zauna ba ya gaji over ya shige falon nasa da yar salamar dake saman leben bakinsa Idannuwansu ne suka sarke da junna a lokacin da ya shigo gaba dayansa Tsadaden murmushi mai sanyayar da zuciya ta dakar masa daga tsayen da take sannan ta nufo shi da yannayin taku irin nata cike da girmamawa ta dan gyara doguwar rigarta ta baza alkyabarta a kasa ta sada kanta sosai a sanyaye ta furta" Barka da karasowa ITIFAL" A hankali ya saki kofar dakin nasa ta dawo ta rufe, wanda hakan ya rufe kallonsu da UMMA ke yi daga nesa Murmushi ta yi ta girgiza kanta ta juya ta koma nasu bangaren, watau bangaren matan masarautar Idannuwansa ya lumshe mata yana sake binta da kallo a lokacin da ta duka har kasa ta saka hannayenta wajen kafarsa ta shiga sulube masa takalmansa dan ta san baya shiga ciki da takalmansa, yakan cire su a saka a wajen ajiyar takalmansa A hankali ta kara dukawa sosai wajen fara kal din safar kafarsa ta kai bakinta da niyar yiwa wajen kisss sai dai baai bata damar hakan ba ya janye kafarsa da dan sauri yana sake wara dubansa a kanta dan ba zai barta ta aikata hakan ba Murmushi ta yi ta mike ta saka hannayenta ta dalube alkyabarsa mai nauyi da masifar kyau ta karasa wajen ratayawa ta ratayata sannan ta juya Da ido kawai yake binta domin bayan ta samu amsa irin ta fatar idannuwansa dan son gane me take yi haka? Ita kuwa cike da takun kasaitar nan tata ta nufi wajen cin abinci tana fadin" Menene bukatar Uban gidana? A nan zaka ci abinci ko a dakinka? Domin burina na ciyar da kai da hannuna ko zan samu albarkar mai Albarka" Jin shirun ya yi yawa dosai fiye da da, domin a da din takan samu dan gyaran murya ko kula irin ta dan sasaukan murmushi ya sakata juyowa itama ta zuba masa idon Sake gyara tsayuwarsa ya yi a tsayen da yake yana harde hannayensa a dake ya furta" ME KIKE YI HAKA?" Ido ta zuba masa na dan sekwani, sai kuma ta sada kanta a sanyaye ta ce" Allah ya huci zuciyarka, shin na aikata laifi ne?" Lebensa na kasa ya dan dantse a hankali , sai kuma ya saki a hankali ya ce" Allah ya saka da alkhairi, ki je bangarenki" Ido ta dake zuba masa, kallo irin mai tafe da ma'anonin da bakinta ba zai iya furta masa kai tsaye ba A harhade ta iya budar bakin nata ta ce" Me yasa kake sake saka nisa a tsakanina da kai? Shekara tara fa ba kwana tara bace" Kafarsa ya daga da kyar ya karasa cikin falonsa ya zauna saman lalausar kujerar falon mai laushin gaske da shinfidar dake samanta ta alfarma dannan ta daga kansa sama yana mai lumshe idannuwansa Karasowa ta yi ta sake dukawa a kusa da shi sosai ta kamo kaffafuwansa ta dhiga cire safar nan sannan ta kama dogwayen yatsutsansa ta shiga matsawa a hankali a hankali tana dan shafa gashin dake kwonce a saman yatsutsan nasa lufluf masu tsantsi da baki A hankali ta ringa yin dan sama da hannayenta tana dan matsa masa kafafuwan nasa tana jin yadda gashin jikin ƙafafuwan ke yi mata susa a tafukkan hannayenta Idannuwanta ta lumshe da ciwo a ranta sosai na yannayinsu ta ce" Bayan na san cewa matsalar mijina a kaina kadai take da tasiri? Me zai hanna yauma mu kwatanta ko maganin da ake nema ya yi anfani? Ina tunanin irin yadda ake rokon Allah a lamarin ta yiwu a yau mu samu magaji?" Kafarsa ya janye a hankali ya dago idannuwansa da sukai masa ja Da kyar ya iya budar bakinsa a hankali ya furta" Ki tafi bangarenki" Kai ta sake sadawa tana hadiye hawayenta sannan ta mike a sanyaye ta nufi hanyar fita tana rufa alkyabarta a saman kanta tana rike kukan da ya zo mata dan kar ta yi a gaban tarin bayin bangarensa da ba kasafai suke kwonciya ba A hankali ya saka hannunsa ya ringa warware rawanin dake nade a fuskarsa har sai da ya dauke shi baki daya sannan ya sauko hular da aka dora masa aka nada masa rawanin a saman kanta Gashin kansa baki sidik irin na bugaje ne ya warware daga nanadewarsa ya sauka a saman kafadunsa haka kuma sajen dake gefe da gefen fuskarsa mai baki da lufluftu ya wanzu a saman fuskar tasa da tsararen halitar fuskar A hankali ya dago fuskar tasa, nan halitar ubangiji mai cike da kamala da tsari ta bayana, watau kyan halitar fuskarsa har zuwa kan jajayen lebensa dake walwali da dogon karan hancinsa wanda ya tafi har kusan girarsa mai cika fa baki a tare da ita sai razananun idannuwansa da suka dauki ja da kallo irin na hatsarin gaske wa'inda suka kawatu da gazar gazar din gashin ido masu duhu da kyali Lebensa ya dake dantsewa, alamun maganar dake cikin zuciyarsa mai cin zuciyar ne, watau mai zafi ce a cen kasan zuciyar tasa ya mike tsaye yana saka hannayensa ya cire babar rigarsa sannan ya cire karamar ya rage masa dogon wandon shadar dake jikinsa fari kal sai dan shatin wando irin na maza na ciki baki wanda kana iya ganninsa ne ta cen saman tsatsonsa a lokacind a ya mike tsayinsa yana lumshe idannuwansa ya nufi baban dakinsa da tafiyar nan tasa tamkar wanda bashida laka a jikinsa Bayi ya zarce direct yana idasa sabule dukkan wani abu dake sutura a jikinsa sannan ya shige cikin ruwan jakuzi mai hasken blu da aka hada da turaran ruwa na wanka mai sansanyan kanshi da dumi daidai misali ya zauna a ciki har gashinsa ya shige ya lumshe idannuwansa yana sake jin halitar jikinsa dake murde masa tamkar wace zata iya aikata masa wata tsiyar, bayan idan har ya fito da ita a haka ya tarbi wace take da damar karbarsa yanzu zata lange ta koma tamkar lagwami......? Wannan abin na ci masa tuwo a kwarya, haka kuma shine gagarumin matsalar da ya kasa daukan mataki a kanta, domin ya fi a irga ya nuna zai sawakewa iyalinsa dan kar a shiga hakinta ama firrr an tare gaba an tare baya, ita dinma ta kafa kai da kasa ta nuna ita ba dan wannan take tare da shi ba, bayan yau da gobe kayan Allah ko a yanzu shi yana hangen cewa matarsa ta kawo gabar nuna bukatuwarta a lamarin nan, kawaicinta na iya karewa wata rana, idan har sanadiyar haka ta fada halaka shin WANENE SILA?, tun bai yarda ba cewa aikin sihiri ke tare da shi har ya yarda bayan dogon bincike na kwararun likitoci da tabatar masa lafiyarsa kalau, a dole ya dawo yake sauraron SHEIK, domin lamarin abin duba ne, har yanzu kuma shiru, shi bai san dadin abin ba, ita bata sani ba, wannan makanta da me ta yi kama?........... Mikewa ya yi ya fito daga cikin ruwan ya karasa kasan shower ya tsaya lokaci daya yana danna ruwan sanyi dan baya so ruwan dumi ya dakeshi sannan ya sake lumshe idannuwansa Sai da ya dauki lokaci a cikin bayin nan ya fito ya cenza kayansa Shi dake dauke da muguwar gajiya, maimakun ya nemi waje ya kwonta sai kawai ya fice ya shige dakin Gymnastics dinsa ya rufe a hankali ya karasa wajen yar karamar redion dake ajiye ya danna karatun Alkur'ani ya karasa wajen injin gudu ya hau ya danna ya shiga gudun da dukkan jarumtar da Allah ya bashi, wace idan har ka dubeshi a haka ba zaka taba yarda cewa wai UMUGHLUK ITIFAL ne a haka , watau *ASADEEK BRAHAM* ______________________________________ Karfe goma na safe ya fito daga bangarensa, da yannayi irin na dan gagawa Ja ya yi ya tsaya sakamakon kanwarsa da ta karaso da sauri jikinta na rawa ta zube kasa muryarta cikin alamun Kuka kuka ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣4️⃣ Ja ya yi ya tsaya sakamakon kanwarsa da ta Karaso da sauri ta zube a gabansa, yannayin nan nata na kulun mai tafe da alamun tashin hankali wanda magabatansu suka tabatar masa ciwo take fama da shi, wanda ya kaita asibitin, haka kuma ana yi mata rukiya ama abin sai a hankali, harta zama da mijinta na neman gagararta domin abin rikicewa ya fi yi ba sauki ba Muryarta na rawa, alamun kukan zata fashe da shi kanta a kasa da jajen da ya zamto mata jiki ta dago rinanun idannuwanta da sam bata samun isashen barci da su ta zuba a saman fuskarsa Mruyarta a raunane ainun ta ce" Aba?" Idannuwansa ya lumshe, yana jin zuciyarsa na dokawa da karfi A hankali ta fashe da kuka tana sada kanta, kuka ne take yi wanda idan har ka dubeta zaka gane akoy abinda ke damunta, gaba daya baiwar Allah a birkice take, tarin dukiyar gidansu da sarautar gidansu bai hadata da komai ba fface tashin hankali da rigingimmun rayuwa, gaba daya ana kallonta da haka ne ana danganta hakan a matsayin dan ta wayi gari ta ga gawar umansu gangar jikinta rabe da kanta ta samu tabuwar hankali, babu wanda ya san menene CIWON wannan baiwar Allah Kukan ta idasa fashewa da shi, wanda ke hadasa masa hauhawan jinni da tashin hankali A hankali ya sake rintse idannuwansa a hankali ya duka, lokaci daya dogarin da ya shigo dan tabatar da fitowarsa dan su gyara abinda zai kaishi filin jirgi ya tafi garin dogon dutsi da suka wayi gari a safiyar yau ba gimbiya ba danta hankali tashe ana nemansu baki dayansu wanda a yanzu mijinta da kansa ya bada umarnin idan aka gansu a kawo su baki daya masarautar garin agadez dukkan hukuncin fa ya hau kansu a zartar, dan kuwa ba zai yarda ta jaza masa masifa ba yana zaman zamansa Da sauri Dogarin ya tare hanyar shigowar yana hakimcewa a dokin kofar Hannayensa ya saka a hankali ya dagota Bai ce da ita komai ba har sai da ya dangantata da doguwar kujerar falon a hankali ya zaunar da ita sannan ya zauna ya kuma riko hannayenta duka biyu yana murzawa a sanyaye ya ce" Autana? Menene? Kin ji jikinki kuwa? Zafi sosai, me kike so ne?" Shigowar UMMA ya saka Auta saurin sake damke hannunsa sannan ta nemi shigewa jikinsa tamkar wace ta ga wani dodo UMMA ta karaso tana rage tsayinta sosai, cike da iya tafiyar da wanda ta saba ta shiga kawo masa gaisuwa sannan ta tambayi lafiyarsa tana hankalce da Auta da abinda take yi Auta muryarta na mugun rawa tana sake shigewa jikinsa ta ce" ABA, dan Allah ka maida ni gidana ka ji?" "Wani irin gidanki za'a maida ke a haka Auta? UMUGHLUK yayanki ne ba abanki ba kulun nusar da ke nake yi, ki dauki dangana kin ji babyna?, Zo nan zo mana jikina na rarasheki yar autana kin ji?" Ta fada tana mika hannunta da nufin janyo autar Da sauri Auta ta doke hannun UMMA tana sake shigewa jikinsa, sai dai wannan act da ta yi ya saka shi dakatar da ita yana nuna bacin ran da yake ta dannewa , da dan kausashiyar murya ya ce" Hey, UMMAN kike dokewa hannu?" A dan zabure ta dago tana kallon idannuwansa domin a cikin rawani yake , fuskarsa a boye take Da sauro UMMA ta ce" Aa ka barta dan albarkana, ka san yannayin jikinta, ai takan min hakan sai a hankali zata daina in sha Allah, ka tashi ka tafi uzurin gabanka ka ji? Allah ya tsare , zan kula da komai nata kar ka damu ka ji? Ka san yannayin jikin da ya zamto haka sai a hankali" Idannuwansa ya dake lumshewa cike da gamsuwa da maganarta A hankali ya ringa bambare hannayen Auta dake kallonsa tamkar zata summa, wani irin kallo mai tafe da tashin hankali da firgici har ya gama zarewar shima yana kallonta da tarin tausayinta a zuciyarsa ya juya ya karasa ya yi gyaran murya aka bude ya fice a falon gaba daya Jikinta ta hade, ta sada kanta tana wani irin makyarkyata da jikinta mai nuni da a birkice take Murmushi Umma ta yi tana dora kafarta daya kan daya tana kadawa Kai ta cira tana jan zaren alkyabar dake jikinta a kausashe ta ce" Dama zaki ba kanki lafiya, ki aminta da maganin samun lafiyarki? Ke kin san menene zaki yi ki samu lafiya, idan har kika ci gaba da naci, da nuna mini taurin kai, kina ji kina ganni yayanki da ya fi kowa sonki zai ci gaba da yi maki kallon mahaukaciya!, Ba kuma zan taba bari a fitar da ke daga masarautar nan bama bsle har wani ya kalleki da mutunci, haka zaki wulakance ki lalace har ki kashe kanki!, Ki sani mulkin wanda kike kira ubanki kayadade ne, takaitace ne!, Muna nan kamar yadda kika ganni da alkyaba bayan ban gada ba gaba da baya, zaki ji ana kirana gimbiya........ Ki ci gaba da yi min taurin kai, zaki kwashi kashinki a hannunki yarinya!" Kanta ta dago tana kamo abin hijabinta tana dake rukunkumeshi a jikinta tana kallon Umma, abu daya take ji a zuciyarta a kan matar nan shine tsana, tsana mai tsananin gaske, sai dai abin tashin hankalin ko a cikin zuciyarta bata isa ta furta cewa Allah ya rabata da Umma ba, sai dai ta ringa Adu'ar A'lah ya rabata da wannan masifa dake damunta......., Idan ta budi baki a yau ta fadi wacece Umma ta tabbata yayanta ne zai fara soketa da ranta, bale jama'ar fada da kowa ke son UMMA saboda munafurcin da ta kware a shi ta iya siyan kowa? Bata tunanin akoy wanda zai yarda da maganar dake cikin bakinta, sai dai ta janyowa kanta balakin da ya fi karfinta, ita bama mutuwar take tsoro ba a yanzu, ta mutu ta bar matar nan a tsakanin yayanta da jama'ar garinsa!, Idannuwanta ta sake rintsewa hawaye na zubo mata tana ji Umma ta mike ta fice A hankali ta sake bude idannuwanta ta kankame jikinta ta budi bakinta dake bari ta ce" YA ALLAH, KAINE GATAN BAWANKA, KAI KA SAN ABINDA YAKE BOYE, KUMA KA SAN WANNAN MATA NA NEMAN FIN KARFINA YA ALLAH, SAI DAI NA SAN KANA NAN KUMA KANA AMSAR ADU'AR WANDA AKA CUTAWA, YA UBANGIJINA KA RABANI DA WANNAN MASIFAR DAKE DAMUNA, ALLAH KAR KA DAUKI RAINA A WANNAN HALI YA ALLAH....." Ta karashe tana sake fashewa da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro................. ____________________________________ *Kauyen LABA, nesa da gari kadan daf da kogin garaje* A hankali take kara yin dage a saman yatsutsanta masu dauke da dogwayen yatsu da faratunna masu dan tsayi da haske tass, haka kuma kafarta ta hagu daure da wata sarka fara kal ta azurfa A zabure kawarta ta mike tana sake dafe kanta da hannayenta biyu, kirjinta na fokawa fat fat fat tamkar itace ta goce zata afka a kogon nan Karkacewa ta yi tana bin yadda kawar tata ke yi ta rike igiya da sauri tana dake zarro ido Bata daina sake dosar kwaduwar dake cen tanakula irin na kwadi ba, haka kuma numfashinta a sama yake sosai dan idan har tga afka a wannan kogon itama ta san sai ta ci ubanta a wajen nan Ido kawar ta rintse tana sharce zufa ta ce" ki yowa Allah ki juyo hakanan, ki bar kwadin nan haka, le wai kwado halal ne kuwa?" Dara daran idannuwanta ta sake zarrowa ta juyo tana dora yatsarta a saman lebenta ta sake furta" SHIIIIIIIII, idan kika yi na afka a ramin nan kin san Hindu sai ta karar da danginku kaf, domin ba zata iya rayuwa babu ni ba!" Shirun kuwa ta yi, domin koda da wasa a tsakaninsu akoy kanshin gaskiya, dan kuwa a jiya har magariba ta sanyo kai ana masifa tsakanin Hindu da kanwar Babar mijinta, matar ta zo ta fadawa Hindu ta daina tura mata aljanar yarnan tata, domin mijinta idan ta shigo masu gida har ta fita bashida abin yi sai kallonta, yarinya ana neman koya mata karuwanci, Hindu ta dauki tafin hannunta mai dauke da yan yatsu biyar ta kifawa matar mari wanda nan da nan garin LABA ya dauka aka yi ta masifa da kyar wutar ta mutu, domin tace ba zata iya hakura a mari daya ba, ita kuwa tace sai dan yayarta ya saki matarsa, shi kuwa yace atafau bai ga abin saki ba a kan dan mari bayan da gaskiyar Hindunsa! Ledar dake kugunta ta dauko ta bude tana murmushi ta dan duka da nufin kwashe kwadin dake tatare a waje guda kamar an hade su anai masu nasiha Ta kawo hannu zata famka wani bakin maciji ya damki guda a bakinda Ihu ta saka ta watsar da ledar, a haukace ta juyo tana takawa da wani irin sauri ba kamar na dazu ba nan da nan sai gata ta tsalako bakinta na fadin" Baki ne a cen, baki ne wawa zai hadiye kwado bai dan ajalinsa ya hadiya ba!" Takalmansu kawar tata ta kwasa ta kwasa a guje , itama ta mara mata baya suka fala da gudu kai kace wasu yan kannanun yan mata ne Basu zame ko'ina ba sai karkashin bishiyar da suke hutawa suka zube sunna ihu da kyakyacewa da daria Kawar tata ta ce" Yau da jarabarmu ta haifar mana da Da da ido!, A yau sanadiyar neman soyawa Aminunki kwado da mun tafi lahira !" Daria take yi har tans dafe shafafen cikinta , hakan ya bayanar da wushiryar dake tsakanin hakoranta na sama yar siririya da kuma dumple din dake gefe da gefen kumatunta tana numfarfashi tamkar zata summe itama ta ce" Yanzu yaya zamu yi kennan? Aminu fa a jiya a dandalin lami da idannuwana na ga yana siyan naman Habu!" "Wai ke naman kwado halal ne?" Kawar tata ta fada tana dafe haba Hannayenta ta watsa ta ce" an dai ce dukkan halitar dake kasan ruwa halal ne, bama a yankawa ai" Kawarta ta kama haba ta ce" Dankari, toh shi kwadon a cen kasan ruwa yake ko yayane?" NADIRAH ta yi tsai, sai kuma ta ce" Kin ga dan Allah kar ki hafen tunani kin ji?, Ai kawai nama nama ne, ni dai takaicina abin kauna ya siyo nama a titi, yo aikin me nake?" Murmushi ta yi ta ce" Kin san menene? Na tabata idan kika dafa masa kwado fushi zai yi da ke, kwado fa" Itama murmushin ta yi tana mikewa ta zauna da kyau sannan ta janyo fararen kafafuwanta da suka yi budu budu da datin farar kasa ta ce" Na tabata zai sauka da wuri, ya kuma san a kan SO NE" Kai kawar tata ta girgiza tna dafe habarta ta ce" INDIRAH, lokuta da yawa idan na ga kunna soyewa ke da Aminu sai na ji tsoro ya kamani, ina tsoron furucin mahaifiyarsa da tace sai dai idan bayan ranta, wai me yasa suke aiki da halitarki suce idan kyau ya yi yawa masifa ne? Gaskiya ana cenfe cenfe a ruga!" Itama murmushin ta kuma yi, murmushi mai matukar karbar fuskarta, ko an fada mata yana yi mata kyau ne ya sa take karra bashi mahinmanci du idan zata yi?, A hankali ta janye dan tsinken da ta nade nanadaden gashinta da shi ta sokashi a cikin kasa ta dubeta ta ce" To idan ta mutun ba sai a yi ba?, Ban san me yasa nakeda bakin jinnin wasu mutanen ba, kema da ba dan kin raina kaka ba da ba zamu yi kawance bafa, an ce mata ina iya dusashe tarmamuwarki in muna tare, ba za'a ringa ganninki ba sai ni kadai?, Ni dai abinda na dani a kan AMINU daya ne, iya rai muna tare, ko na kashe shi ko ya kasheni ba zan iya rabuwa da shi ba, domin tun ban iya so ba har ya koya min.......... Na tabata yana kofar godan Hindu tashi mu karasa na ga ABINCIN RUHINA kin ji? Mamansa kuwa ta sake daure kugu da kyau, idan muka buga mata muhamada a zo a kada kalangum daurin auren danta da ni!" Ta karashe tana janyo takalmanta ta saka na hannun hagu din, da na damar ta dake wani katon kadangare da ya nufosu gadan gadan ta jefar da shi ta saka takalmin sannan ta janye abinda ta soka a cikin kasa ta sake hade gashin nata a tsakiyar kanta ta nanade ta soke sannan ta nufi wajen kawarta watau RAMA suka dauki hanyar gidan KANWAR MAMANTA watau HINDU shagali. A tsaye suka tarar da ita, ta sha wani irin daurin zani wanda ya haura cen saman kaurinta , kanta ba dan kwali ta Barbaza gashin kan nata tana tsaye tana rike da kofar dake jikin hanyar shigowa tana leke Idannuwanta na dauka a saman fuskar y'ar yayar tata ta daki murmushi ta mika hannu ta janyota tana fadin" Lalle da yar so yar cikin kirjina, yarinyar da zan wanke na mikawa sarki, dan walahi uban talaka ya yi kadan na bashi yata, na fada na kara, nu har an min iya shege ne a kan yarinyata? Idan da ubanda ya ga a wajen da aka ce dan ta cika kyau maya ce ita ko aljana ya kawo min wajen na karanta, iskancin banza iskancin wofi, yau sai na ci uwar maman Aminunki a garin nan!'' Ido ta zarro a haukace ta idasa shigowar tana kai hannunta ta rufe bakin Hindu tana sake zarro idannuwanta ta ce" Innalilahi Inna me dangin abin kauna suka maki kuma kike zagi so kike ta karra cewa ba zata bani shi ba?" Ido suka zuba mata, daga innar tata har kawar tata, ba za'a bata shi ba? Innalilahi wa inna ilaihi rajune, yau sun ga salwatacen bakon iskanci a wajen NADIRAH! "Ke indirah Hindunta , kar ki ce mun a kan namiji kina iya kuncen zani a kasuwa?, Dan ubanki yanzu uwarsa ta fita ta zo ja min kunne wai kar ki kuma shiga sabgar danta, itafa ba zata taba bari da ranta ki aurar mata da ba , salon ki saka ya manta wacece uwarsa a duniya? Wai sam bama zata iya bari ki shiga ahalinta ba , domin yayansama sonki yake, ke bari ki ji ni kuwa nace ai ubansama yana iya sonki dan kin keru, kuma nima na ja mata kashedin danta kar na kuma ganninsa a kofar gidana ya zo zance, ya kiyayeni ya kiyayi yata, dan walahi a kanki sai na nada mata duka, muma bama so!" Hindu ta fada tana zarro ido da sake gyara tsayuwarta Silalewa Nadirah ta yi a kasa tana cire abin dake soke a kanta ta fadi" Shikenan, na shiga uku na lalace, ku ina ruwanku da soyayarmu ne wai? To guduwa zamu yi idan kuka shiga ciki, mamansa kuwa ai kyaleta na yi idan da rabo ba dai ta je kiyamar ba a yi? Haba Innar Indi ke da kanki? Gaskiya wucewa zamu yi a je a basu hakuri" Kamar an gaurawa Hindu mari a kuncinta haka ta dafe kunci a zabure, sai kuma ta kai hannayenta saman kanta ta fashe da kuka tana fadin" Asalamu alaikum.......fatan kunna kalau? Yaya ake ciki? Yaya kuke gannin ake ciki? Yaya kuka ga salon?........ Shin me yake boye mai zai bayana a rikicin tafiyar labarin UMUGHLUK ITIFAL? WANENE UMUGHLUK ITIFAL ASADEEK BRAHAM? ME YAKE FARUWA DA KANWARSA YAYA LAIFIN DAKE CIKIN GARIN TANUT? YAYA ZAI WARWARE? ME KE TAFE DA ZUCIYARKU DANGANE DA NADIRAH, WACE AKE KURA DA INDIRAH, YAR GIDAN FADIME DA INARTA HINDU? .............. BAN FARA DAN NA DAINA BA IN SHA ALLAH KUMA FREE NE.......LADAN BIYANKA KAWAI COMMENT NE 🥰🥰🥰🥰🥰🥰 *Yar uwa, shin kin sayi labarin kwatena mai taken CARBIN KWAI?, idan bali siya ba lalle zan iya kiranki mai wasa da dama, carbin kwai shine ke tafe da abubuwan da zaki iya fadowa daga saman gadonki dan dariya da farin ciki, akoy abin tausayin, uwa uba cakwakiya............CARBIN KWAI akoy ilimantarwa, tunatarwa, nishadantarwa, ke harta motsin gado😁, ki dai garzayo kawai hajiyata tuni mun fara posting a naira 300 kacal ki samu naki ki more* *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣5️⃣ *Wai kun siya kuwa? Ku fa zo ku samu naku, takensa shine CARBIN KWAI na KWATENA, kawata , maman jariri, wannan marubuciyar BADAKALA na AMMAR dan aljannah, da kuma BAIWATA mai lulube da baiwar alkhairi......., Ba zigi a ciki ba kuma kodawa irin ta mai siyarwa, idan ka siya sai ka ji tamkar ka karra ninka mata kudin dan farin ciki da jin dadi.....MALAMAR hazika ce mai baiwa a lulube a tare da ita....... MAZA GARZAYO KA SAMU NAKA A FARASHI MAI SAUKI 300 NAIRA* Hindu ta fashe da kuka tana kallonta ta ce" La ila ha ilalahu muhamadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallam, yanzu Indin Hindu ni zaki tisa mu koma na baiwa matar da na gama yiwa alkawarin yata sai saraki? Ke wannan yarinya ki raba kanki da lamarin maza, ke yanzu wace irin soyaya ce zata saka ki gudu da kato ki barmu da abin kunya a NIJAR? Kar ki manta wanene ubanki a gidan sarkin garin TANUT, kar kuma ki manta wacece mahaifiyarki a fadar matar mai Garin TANUT!, Ni din nan kin san wacece ni, kuma ki wulakantamu haka? Ko dai magani ya yiwa y'ar nan ne wannan shegen langayayen yaron?" NADIRAH ta kwabe fuska, sosai ta nuna daf take da yi mata kuka ta ce" Ba zaki je ba dai ko? Imnata ba zaki je ba? Ai shikenan Innata ki yi zamanki, ki zauna idan Aminu ya tsaneni duniya zan bi Innata, ki zauna, kuma kin sani sarai a duniyata ba ni ba maganar ratse ta hanyar da sarki ya bima bale wai ni na kasance a innuwa daya da sarki, Innata ko sarkin yan iskan garin nan aka aura min in dai sunnansa sarki in sha Allahu ko gawata aka mika sai ta yi fatalwa ta dawo da kafafuwanta, me ake da rayuwar sarauta rayuwar matsi rayuwar rashin barkatawa kai abin kirki? Kana zaune tamkar duwawu komai sai an yi maka? Innata ki daina yi min mugun fata kin san fa uwata ce ke ko?" Sai kawai ta karashe tana mai fashewa da kuka harda kwonciya a nan wajen ta dora kanta gashinta du ya shige cikin kasa Tsuru tsuru suka yi, daga innar tata har kawarta sunna kallonta Innarta ta sake dantse lebe, ita kam jarabawarta a rayuwa kaunar yarta ne, a duniya bata iya cewa NADIRAH aa, walahi tana iya yin ba dadi da mijinta ta kwonta kalau abinta , ama idan hankalin NADIRAH a tashe ko ruwa bata iya sha, tunda yayarta ta haifi yar take jin tamkar ita ta nakudo abinta ta haifo, shi yasa harta sunnanta yan gari suka hade suke kiranta INDIRA wasu suce HINDIRAH, domin a bayane soyayarsu take ba a boye ba, soyaya irin ta uwa da d'a, a kan Nadirah fa ita sai ta zagi mai rabo walahi ko uban wanene! A hankali ta dubi Kawar NADIRAH ta ce" Ki kamata mana kema kina kallonta?" Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" Inna kin san halinta sarai fa, bafa zata saurareni ba" Inna ta sake sauke ajiyar zuciya ta kunce mayafinta ta yafa a saman kanta ta duka tana rike hannun NADIRAH ta ce" Shikenan, tunda so kike a raina maki uwa salon gobe idan an zo taron auren naki ace uwar taki wacece ita yo a wajenki tashi mu je, ama kar ki manta bafanki bai san zan fita ba, kuma kin san ba kyau matar aure ta fita mijinta bai sani ba ko?, Sannan kuma idan muka je na bada hakuri an kama maki gori kennan, Haba ta Aminu, haba aminar Aminu?, Idan kika yi hakuri da kaina zan raka ki dandali na ba Aminu hakuri ku ci gaba da hirar tsakiyar ranarku kin ji yar arziki irin albarka?, In kuwa kin fi so mu je din mu je kawai sai na dukama na bata hakurin ai ba komai rayuwa ce dan an min gori an zagi innarki ai ba komai" Kukan nata ne yaa rage tana kallon Innarta Innarta ta ce" Yi shiru tashi ki daina kukan, in dai dan tisa keyar uwa ne a kaita ta bada hakuri ai ba yau ba kika fara, yau kika fara kaini na bada hakuri idan mun yi fada da mutane ne? Tashi mu je Allah na tuba mai bada hakuri ai shine dan aljannah!" Manyan idannuwanta ta kikifta, sai kuma ta sada kanta bayan ta dago shi tana kakabe kasar dake kanta, haka kuma ta yi shiru da kukan da take yi A sanyaye sosai ta ce" Innata, baki yi tatsa ba?" Hindu ta yi murmushi ta ce" Haba dai ai ba zan zauna har ki dawo ban yi tatsa ba, bayan na san shine abincinki, gayacen cikin kwaryar cen a lulube da saki dan ya kara sanyi" Murmushi ta yi itama ta mike ta karasa wajen kwaryar ta zauna ta bude tana sake sakin murmushi, domin an shake mata kwaryar sosai Gaskiya ba zata kai innarta ba innar Aminu hakuri ba, matar bata son zaman lafiya, me yasa ba zata yi hakuri bane wai? Kulun sai ta zazageta , da a iya ita ta tsaya lafiyar Allah ba zata fadawa Innarta ba, ama ta taso ta tardo inna? Bayan in dai a kanta ne inna batada hakuri? Sam bata kyauta ba walahi, ama ba komai zasu hadu da Aminun ne, bara ta sha ta koshi ta yi shirin dandali, ta tabata bawan Allah shi yau bama zai iya cin komai ba, ai idan suka yi fada tamkar zai muti yake dawowa, aminu kennan aminin arziki abin kaunarta!................ ___________________________________ Tafiyar jirgi suka yi, zuwansu da dawowarsu, hakan ya sa dudu basu wuce awani biyar ba a tafiyar tasu da zamansu da sarkin garin da kuma dawowarsu garin AGADAZ, domin tafia ce ta takaitacen lokaci a jirgi Kana gannin fuskar Mai garin Agadaz zaka fahimci yana cikin wani hali, domin fuskarsa ba alamun ya taba yin daria, duda a cikin rawani take, ama haka zaka iya fahimtar hankalinsa ba a tashe ba Sallar la'asar suka gama a baban masalacin fadar, ya zamto kusan kowa ya watse sai shi sai Sheik Kansa a sade yake yana jan carbin dake hannunsa a hankali ya sake duban Sheik dake magana a sanyaye Ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya ja rawanin dake saman fuskarsa ya dake mayar da dubansa saman makarar dake ajiye a cikin masalacin sannan ya sake duban SHEIK a nutse ya ce" Wanene ni, da za'a ringa maimaita min cewa Mulkina takaitace ne? Da ni din wanene da zan shagala cewa mulkina dawamame ne? In ba shirme irin na Bafana ba da ya fitar da maganar nan wace tale sirrina ce har ta fito daga cikin gidansa ta yadu a wajen da ban shirya jinta ba dama me zai sakani ni bawa da Allah ya halita dauka cewa zan zartar da mulki a doran kasarsa dawamame? Wai su basa tuna mutuwa ne? Ko sunna manta wanene mai Mulki? Mu jagoranci ne muka samu na talakawa, mai mulki shine ALLAH, Yah SHEIK, dan kawai ina kamanta adalci sai na zama abin farauta?" "Ka yi hakuri ALLAH ya taimakeka" Sheikh ya fada a sanyaye, domin shima abin nan ya dake shi, jakafiyar matar sarkin garin Dogon dutsi ce ta miko sakon da akace ta bada, tana kuka tamkar ranta zai fita cike da tsoron kashedin da aka yanka mata a kan ahalinta, sako mai dauke da takarda fara mai dauke da magana kamar haka *ka yi zamaninka, iya damarka kennan, ba zamu bayana ba sai lokacin da ka gushe, domin kai la san sarautarka takaitaciya ce, kai da baka iya saka kukan jariri a gidanka ba bale a yi tsoron dan tsako ya giga?, Ka yi ta kanka kawai domin ka sani yanzu kakeda abokan gaba!* Numfashi ya sauke mai zafi ya ce" Ka daina ce min Allah ja da zamanina idan muna daga ni sai kai SHEIKH, ka dubeni kawai ka fada min gaskiya!" Sheik zai yi magana aka nemi izinin shigowa bayan an yi salama Kasancewar sun gane mai son shigowar ya saka Sheik ya bashi dama Kasa ya duka sosai kansa a kasa ya ce" Allah ya taimakeka, sako ne daga Bafanka, a kan maganar zuwansa dan son ganninka, yace da da hali kafin ka yi tafia" Shiru ne ya biyo baya, shiru mai tsayin gaske, sai da ya gama tunaninsa sannan ya sake dantse lebensa a kausashe ya ce" An bashi dama" Sheikh ya kalleshi da sauri, ya raka Dogari da kallo ya sake dubansa A tausashe ya ce" ASADEEK, ka san rigima ce ta cikin gida ko?, Kar ka daukaka abin nan , ka yi hakuri ka ji?" Rawanin da ya sasabto kada ya ja a hankali ya mayar ya rufe har wajen hancinsa da shi sannan ya duba agogon hannunsa domin ba zai shiga gida yanzu ba sai ya gama karatunsa an gama salolin da suka rage , to mema zai shiga ya yi ne? Ya tabata Auta tana nan bata yi barci ba , rigimarta na nan tare da ita, matarsa kuwa bai san me zai je ya nema a wajenta ba tunda bashida abinda zai bata, yana so sai ya je ya dawo daga tafiyar nan zai zauna da ita, zasu yi zaman da ya dace, zai yi kokarin kwatanta mata abinda ya dace ta fahimta, sannan zai yasare mata wahalar da yake gannin tana tare da ita, domin shi dai wada yake ciki shi kadai ya san ukubar da yake ciki, baya rabo da ciwon mara, tamkar zai kashe shi wani lokacin.....ama ba komai Allah ne gatansa Dare ya cika sosai a ranar nan, domin sai kudan karfe dayan dare suka doso babar farfajiyar ta masarauta shi da makarabansa, mutun takwas sunna tafe cikin nutsuwa, haka kuma sun sakashi a tsakiyarsu Dakatawa ya yi yana duban dogaransa mutun hudu,da dima diman bodyguard dinsa mutun hudu, watau masu rike da bindiga Dan murmushi ya yi wanda bai yi tunanin a yau zai iya samunsa ba sakamakon irin bacin ran da ya hadu da shi, sai dai zama a cikin datijai da zikirin da suka yi ya sanyyayar masa da zuciyarsa harma yana jin a yanzu ko wani hukunci ya yanke bafa da bacin rai ya yanke shi ba, ba zai yi nadama ba "Duba ku ga Namiji har namiji, sai dai ba husssss.................." Ya fada daga saman dakin da ya sauka, watau bangaren bakin ahalin gidan, baban dakin da yake nasa a matsayinsa na bafan Sarki Abinda ta saka ta kare fuskarta ta sake ja ta rufe fuskar tata sosai itama ta karaso wajen labulen ta tsaya tana kare masa kallo, alkyabarsa sam bata boye cikar halitarsa ba, bama zakak gigice ba dai ka ganshi ba alkyabar, domin du wani bayanannan abu da Gymnastics ta haifar masa a jikinsa kan bayana ne, bai yi irin wannan bulewar ba har ta baci, ama wace ya yinma a nan kusa dai babu ginanen namiji irinsa sai dai a nesa Ajiyar zuciya ta sauke ta fita daga wajen labulen ta koma saman kujera ta yaye lulubinta gaba daya tana kallonsa ta ce" Munaa cikin gagarumar matsala, shirunsa da rashin hargaginsa ba yana nufin bashida kulaliya a zuciyarsa ba! Ni na raine shi, ko mahaifiyarsa ba zata fada min wanene shi ba!" Labulen Bafansa ya saki cike da jin kishin yaron da tarin kasar da Allah ya tara masa a cikin zuciyarsa ya koma ya tsaya kikam a saman kanta A amon muryarsa zaka gane ransa a bace yake ya ce" Yanzu ace, daga jin wannan magana ta bila na kasa zaune bale tsaye sai da na kawo kaina? Ni da nake bafansa kennan? Da wani ne fa?" Baki ta tabe tana duban agogo ta ce" Ba zaka gane ba, kasancewarka bafansa a idannuwan talakawansa kadai ka tsira, summa dan basu san wanene kai a rayuwarsa bane, ka ga ASADEEK? Yanada mugun daukaka a idannuwan Agadasawa!, Da ace maganar nan gari ta zaga da yan cikin garinka zasu fara kai maka farmaki !, Yanzu du ba wannan ba, da me zaka tunkareshi a goben?" Zaunawa ya yi yana fuskantarta ya ce" Da me zan tunkareshi kuwa? Tunda na taso na zo da kaina zan bashi hakuri ne kawai na koma komai ya wuce, abinda gimbiya ta aikata kuwa na mata kashedi ta min alkawarin ba za'a kuma ba" Ido ta zarro tana kallonsa cike da mamaki Da dumbin mamaki ta ce" Anya zaka iya mulkar garin Agadaz nan gaba?" Da bacin rai ya ce" Ki gyara furucinki a kaina , kar ki manta wacece ke?" Bakinta ta tabe tana cire kanta, muryarta da haushi haushi ta ce"Kaima kar ka manta me yake tsakanina da kai? Kafin ka ffara tunanin watsar da ni ka tuna da me da me zaka yi wasa!, Maimakun ka tambayeni dalilin furucina sai ka hau kan isa da iza bayan magana muke a kan SARKINKA?" wannan karron kasa ce mata komai ya yi,dan babu abinda ya fi kona masa rai irin ya ji an kirayi yaron bayansa a matsayin sarkin da ya fi shi fada a ji! Ajiyar zuciya ta sauke ta saisaita muryarta ta ce" Ka yi hakuri, ina so ka fahimci girmann laifinka, sannan mu samu mafita, ka sani idan bamu yi da gaske ba neman gira ne zai saka mu rasa ido, kar ka manta namiji kake, yaya zaka ji idan talakanka ya zagi mazakuntarka? Uwa uba a gaban wani dake kasa da kai? Zarafinsa aka ci, mutuncinsa aka ci, dole a samu hanyar da za'a wanke kai, kuma a wanke shi a idannuwan wanda aka zageshi a gabansa!, Dole zaka duka a gabansa ka nemi kanka, dukawa wada baya hannawa a mike da tsayi, ka fuskanci furucina ka samawa kanka sauki, idan har ba haka ba zaka sakawa kanka damuwa ne!" Ikon Allah shi yake kallo, ransa a matukar bace ya mike daga zaunen da yake ya nuna mata hanyar fita a kausashe ya ce" Kin ga, tashi ki tafi" Da mamaki take kallonsa A tsawace ya ce" Na ce ki bace min da gani, tunda a yau ni zaki zagarwa mutunci ki dubeni ki ce na je na dukawa yaron da na haife shi da cikina? Tashi ki tafi!" Murmushi ta yi mai ciwo da ma'ana da dama a zuciyarta, tabas idan ta daki kirji ta ce ta fi kowa sannin wanene UMUGHLUK ITIFAL bai dace a yi mata gardama ba A nutse ta mike, cike da ita ta gyara hijabinta da yannayin shiga irin ta bayi dan yin bada sau ta sake rufewa da kyau kasa kasa ta ce" WANDA BAI JI BARI BA, ZAI GA UWAR BARI!" A labe ta fice a boye ta samu ta koma bangarenta ta ringa kai kawo dan bacin rai, tamkarma abin ya fi damunta fiye da sarkin, sam baya gannin abinda take gani, ama ba komai idan da rabon su sake zama sa zauna! Washe gari *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣6️⃣ *Washe gari* Da misalin karfe tara da dori kadan A hankali ya sake debo abincin a cikin spoon ya sake nufo bakinta da shi yana murmushi , cikin tausashiyar muryarsa kasa kasa sosai ya ce" To naji, zaki bi ni ko? Ha sai kin koshi tukunnan kin ji?" Idannuwanta ta lumshe, idan yayanta na irin abubuwan nan takan ji hankalinta na sake tashi, idan ta tuna dukkan abinda yake yi a kallon mahaukaciya yake yi mata irin a lalabakan nan, sai ta ji duniyar baki daya ta fice mata a ranta Yawun bakinta ta hadiye ta sake bude bakin nata ta amshi abincin a hankali ta ringa taunawa still tana kallonsa Murmushi ya yi yana sauke ajiyar zuciya ya dauki tissu ya goge mata bakinta sannan ya dauki ruwa mai dan sanyi sanyi kadan ya nufi bakinta da shi A hankali ta amshi ruwan, ta fara sha kennan aka shigo da salama Kwarewa ta yi da ruwan dake bakinta da sauri ta shiga tari, sai dai abin mamakin, ba ta tarin da take take ba, watau tana tarin yayanta yana riketa da yi mata sannu da kokarin kafa mata ruwan a bakinta dan ya sasauta ama ita ta rike hannunsa kakam tamkar zata shige cikinsa , lokaci daya kuma jikinta ya dan dauki rawa rawa tana dake kankameshi Da sauri Umma ta karaso tana fadin" Subahanalah, my baby ruwa ne ya kwarar da ke, yarona ka bata mai sanyi da yawa ne? Ka dan bana bata mai sanyi dan yana dakata tari, yannayin jikinta sai ana kula Yarona, fan sako min ita na gani? Zo nan na gani autana?" Da karfi ta dake dantse hannunsa tana rintse idannuwanta hawayen cikinsu suka samu zirarowa daga gurbin idannuwan nata ta kifa kanta a gaban shadar dake jikinsa ta ja numfashin dake nuni daf tale da fashewa da kuka A hankali ya sake zuba mata ido yana nazartarta, sai kuma ya dago ya kalli UMMA dake kusansu sosai Hannun UMMA dake dan taba Auta, Auta na warcewa ya bi da kallo, a hankali ya sake kallon UMMAN wace ke aikin da ta saba, watau nuna mata kauna da tsantsar soyaya Idannuwansa ya cire a kanta yana sake duban Dogari da ya sanar da son shigowar Bafansu, haka kuma ya sake duban Umma Dan murmushi ya yi a hankali ya ce" Yauma fada kika yi da mamanki ko?" Da sauro UMMA ta dago tana kallon fuskarsa, furucinsa ya tsoratar da ita, hakan na nufin ya fara gannin wani abin dake tsakaninsu ne? Watau turetan da Auta ke yi? Dan murmushin yake ta saki ta dan ja da son taba Autar ta zauna tana fadin" Ai ka san halin Auta, ita fa damuwarta a kan shan magani ne, jiya har ta kwonta na tayar da ita , shine aka yi ta kuka da kyar na lalabata ta yi barci" Murmushi ya sake yi bai ce komai ba, domin Bafansa ya shigo tuni yana tsaye yana kallon Auta da irin abinda ke faruwa Dan tsaki bafansa ya yi yana dafe kai ya kai zaune ya ce" ASADEEK , na rasa me yasa ka ki a kai yarinyar nan asibitin masu irin ciwonta, gata abu sai karra yin gaba yale, wannan rukunkuma haka kamar wata yar yarinya bayan mace take magidanciya? Ai gwara ka yi hakuri a kaita a ringa bata magani ko abin ya yi sauki ko?" Jimke hannunsa da Auta ta yi ya saka shi sake dubanta a hankali, domin hakan da ta yi ya sheda masa dayan biyu ne, Au ta ji abinda bafanta ya fada har ya mata ciwo, ko kuma bata son jin muryarsa ne. A hankali ya sake riketa yana sake gyara mata hijabinta dan kar ya shaketa, murya a tausashen da ita kadai yake yiwa magana a haka ya sake talabo fuskarta kasa kasa ya ce" Menene? Bakya so a kaiki asibiti ko?" A hankali Auta ta gyada kanta, sannan ta dago idannuwanta ta dube shi muryarta a raunane ta ce" Ni ba mahaukaciya bace ABAHNA kar a kaini ka ji?" "Ahaf, idan ba haukan ba me zai saka aikata wani aikin yar nan? Yayanki ne fa kike ce masa ABA, ai ke ba magajiyarsa bace, kuma wannan zama haka ai idan ba ana cikin hali na rashin hayaci ba ba za'a aikatashi ba sam" bafansu ya fada yana dan kada kafa Kasa kasa ta dan mike ta dauki jus din dake ajiye ta kai gabansa ta ajiye masa, cikin dabara ta saka kafarta ta take tasa da karfi, harda murzawa sannan ta koma baya ta zauna tana murmushin yake ta ce" Aa fa bafansu, ba za'a kai min yarinya asibiti ba, a nan din ai zata fi saukewa idan tana ganninmu a gefenta, a hankali sai ka ga kamar ba'a yi ba, tunda likita yace ciwonta na dan lokaci ne, damuwa ce ta haifar mata da shi, idan har ta samu kwonciyar hankali ko yayane zata samu sauki" UMUGHLUK dake rike da ita idannuwansa a lumshe, zuciyarsa na tafarfasa ya dan ja hannunsa a hankali wanda ta nitsa masa farce ya sake dago fuskarta ya ce" Auta, kina ji? Tashi ki je ki kimtsa kayanki kin ji? Sai mu tafi ko? Ki shiryasu sosai fa, ki saka harda bruch da maganinki duka kin ji?" Wata irin ajiyar zuciya ta sauke mai sanyi ta mike tana sauri harda hade tafiyarta ta yi waje , wanda ke nuni da kamar wani irin farin ciki ta ji na furucin nan A hankali ya juyo inda Bafansa yake ya dan wara kafafuwansa ya dora hannayensa biyu a saman gwuiwoyinsa ya kai hannunsa wajen gashin kansa dake daure ya fan shafa kadan sannan ya saka idannuwansa cikin na Bafansa , A kausashe ya ce" Bismillah " Bafansa na zarar ido ya dago shima yana sake kallonsa, dan sai ya ji kamar amon muryarsa yanzu ba daya ba da ta dazu A dan rikice kadan ya ce" Dangane da abinda ya faru ne dama jiya na kasa zama nace zan zo" Shiru ya yi ko zai ji ya yi magana? Sai ya ji bai ce komai ba Bafansa ya ci gaba da fadin" Ka san lamarin mata ne da rashin jin magana, ka yafe masu ba zasu kuma ba in sha Allah " Ikon Allah kawai yake kallo, kwata kwata bafansa bashida wayo bale tunani Kai ya fan girgiza yana cire dubansa kadan ya ce" Ok ba damuwa" Da mamaki ya kalle shi, kasa rike mamakinsa ya yi ya ce" Kana nufin komai ya wuce kennan?" ASADEEK ya muke tsaye , gaba daya tsayinsa ya mike a gabansu Dan murmushi ya yi ya dubi Ummansu dake zaune kanta sade kwata kwata bata damu da maganar da suke yi ba, ya tabata ta shigo ne dan a kimtsa masa kayan tafiyarsa, yana son fada mata umura fa ya nufa yana kuma cewa ba zai fada mata ba zai mata surprise ne idan ta je su hade a cen Dubansa ya maida kan BAFANSA a hankali ya ce" Babu wata damuwa ai, Mata ne, bakinsu bashida linzami sai sun samu dorinar da ta daki bangonsu..............., Allah ya takaita ama ina tsoron fushin da dogarai suka dauka, harfa cewa BABAYE ya yi in ba dan bafana kake ba, me ya hauda kai saman karaga bayan dan kaka hajia kake ba dan kaka elhaji ba?" Gabansa sai da ya kwonci kwonci ya fadi har ya mike tsaye cirr daga zaunen da yake hannayensa na rawa Da sauri ya ambaci sunnansa gannin ya juya ya nufi uwar dakansa, sai dai bai tsaya ba Da sauri ya daga kafarsa da nufin binsa, sai dai ya dakata da karfi yana kallonta gabansa naa faduwa Da idannuwanta ta masa nuni da waje sannan ta sake shi da sauri ta fara ficewa ta nufi bangarensa Tana tsaye a dakin tana kai kawo ya bude ya shigo hankalinsa a mugun tashe ya nufota yana fadin " Me wancen marar mutuncin yake nufi? Me yake nufi da furucinsa a kaina?" Da sauri ta karaso ta dora hannunta saman lebensa tana fadin" Shuiiiiit, safiya ce, WA'INDA ke jira yace a yi sun fara bazuwa ka rufawa harshenka asiri kar tun daga nan ya kirayi Sarkin damagaram su tujeka daga kujerar mu shiga uku baki dayanmu!" Yanzun kam tsakaninsa da Allah jikinsa rawa yake Zaune ya kai dan ba zai iya jure tsayuwar ba, muryarsa na rawa ya ce" Me yake nufi da ni? Yaya zan yi kennan?" Idannuwanta ta wanna tamkar wata yarinyar mace ta zauna itama a daf da shi sosai tana kallonsa ta ce" Abunda yake nufi da kai ramuwar gaya ce, abinda zaka yi kuma a yanzu idan ka saurareni ina iya saka ka a hanya!" Fuskantarta ya yi sosai dan haka ta yi murmushi ta ce" INA BAHIJA?" Zufar dake gaban goshinsa ya share yana sake jan ajiyar zuciya yana jin meye na tambayar Bahija bayan ba wannan ya kawo shi ba, ba shine matsalar ba! A takaice ya ce" Tana Hotel zata je Umarah wai bana!, Ki min maganar da kika ce mana" Murmushi ta yi ta sake gyara zamanta ta ce" Dama shawarata a gareka itace, ka sake samunsa wannan karron tare da Gimbiya, ku zauna a saman cafet ku zanta, ka dube shi ka bashi hakuri mai sunnan hakuri, sannan ka nuna masa ka zo da maganar bashi yarinyarka mace kwalin kwal ya aura!" Ido ya zarro yana kallonta Da mamaki ya ce" Lalle yau na fara tunanin ke ya dace ki hadiyi maganin saka barcin nan na wancen mahaukaciyar kanwar tasa ba ita ba!, Kina nufin ni na dauki yarinyata na bashi? Kyan zata zauna kallo har duniya ta nade ne ko me? " Kai ta girgiza tana safe dafe kanta, lalle wannan mutumen babu mahaukaci irinsa, ba kuma zai taba zama mai hankali ba Sai dai tunda so take yi su fuskanci junna sai ta sake tausasa muryarta ta ce" Ka gane inda na dosa mana Aban BAHIJA, kasancewar babu abinda zai iya yi matan na kwadaita mana haka, sannan zamu jefi tsuntsu biyu da jifa guda ne!" Kallon me kuke nufi yake yi mata, dan haka ta sake gyara zamanta ta ce" Ka san menene burinmu, wanda muke fata yaron nan kar ya jima a saman kujerar mulki, idan yau BAHIJA ta zamto iyalinsa hakan na nufin itace mafi kusanci da shi fiye da kowani dan Adam a duniya, ta haka a kwanaki kalilan tana iya kawo karshen rayuwarsa, kai ka gaje abinda ya gada cikin ruwan sanyi ba tare da mun wahala baki dayanmu ba, sannan ta fita ta auri wanda take so ko?" Ido ya zuba mata sosai yana kallonta Bai san lokacin da wani murmushi ya kubuce masa ba, Da sauri ya mike yana fadin" Bara na koma na ganshi yanzuma" Hannunta ta saka ta janyo shi har sai da ya zauna daf da cinyarta, a hankali ta dora hannunta saman cinyarsa ta dan matsa ta ce" Ka manta tafiar yamacin nan zai yi? Ai ba zaka samu kebewa da shi ba kuma , inaga zai nufi kasashen turai ya huta ne, ka zauna kawai zan je na hanna wancen mahaukaciyar binsa, domin idan har ta bi shi komai na iya faruwa, ka bari idan ya dawo sai ku zo da Gimbiya ku same shi, nima zan kasance a wajen kafin lokacin dan na tayamu yaki" Cike da bege ya rakata da kallo har ta gama bada sawunta ta tsaya ta gamsu da hanyar ba mai ganninta ta fita da sauri ta nufi bangaren AUTA Karar bude kofar ya sakata dagowa da sauri daga cusa hijabanta da take yi a cikik akwatinta ta juyo Gabanta ya sake yankewa ya fadi da sauri ta zauna ta hade gwuiwoyinta ta dora kanta a sama tana yin gaba da baya kamar tana zizigar jariri a bayanta , tsoro da faduwar gaba sun cikata Dakin ta rufe da ky ta karasa inda take zaunen nan ta duka cike da takaici ta ce" Ina kike tunanin zuwa? Ama bakida hankali yarinyar nan kwata kwata!, To bari ki ji, idan har kika yarda kika bi yayanki tafiyar da zai yi na rantse maki da wanda raina yake hannunsa kina dawowa zan makala maki mugun sharin da yayanki da kansa zai haka rami ya saka ki kanki a fili sannan ya jefe ki da duwatsu har sai kin rasa ranki......, Ke kin san ciwon wannan zai halaka shi shima dan makahon son da yake maki!, Ta rage naki , ki duba ki ga abinda zai gyara ki!" A hankali ta dafe zuciyarta ta silale a kasa ta dora kanta a saman akwatinta ta rintse idannuwanta A bayane ta furta" ALLAHU AJURNI FI MASIBATI, WA KHALIFUNI KHAIRAN MINE HA....." sai kuma ta karashe tana mai sakin kuka tana jin kanta tamkar zai tarwatse gida biyu A hankali ta sake dafe gaban kirjinta, ita ba waya ba, ita ba komai ba, an amshe , yanzun a barta ta je ta yi ibadar ko zata sake neman gafarar ubangijinta da fatan ta gama da duniya lafiyama ba zata samu ba? Lalle ta fara kulatar mijinta, shin ina yake ya bari ake neman kasheta? Ba zai lekota ya ga amanar da aka bashi ba? Ba zai nemi ganninta ba ko zai karanci damuwarta? Ko dan ta rasa cikin dake jikinta ne ya tsaneta?....... A wannan rana sallah kawai take tashi ta gabatar ta koma ta nade, har lokacin tafia ta yi, tana ji tana gani ta gilawa yayanta karyar juwa take ji ba zata iya tafiyar ba, zata je haji idan Allah ya nufa, tana ji tana gani ya mata salama ya fice tamkar zata mutu dan tashin hankali, sai dai ta sake mayar da kanta ta sha madarar ruwa ta kuma fuskantar alkibla, ta san Allah yana gani, ta kuma san idan bata ga warwarewar matsalarta a duniya ba tabas a kiyama Allah zai saka mata, dan haka sai ta ringa kai masa kukanta tana fada masa yayanta dai, yayanta dai, domin babu babar fargabar da ta kai shi a zuciyarta, idan ta tuna shi takan dimaucewa, takan rasa komai nata, sai idan ta fuskanci gabas ta yi kuka ta fadawa ubangijinta sai ta ji sanyi a zuciyarta, sia ta ji kamar komai normal ne tunda akoy Allah. A cikin JIRGIN VIP, watau wanda ya fara daukan manyan mutane dan sada su da babar kasa, kasa mai tsarki dan gabatar da aikin Umurarsu Cike da kasaita take tafe tunda ta shigo Daidaikun mutanen dake dan yi mata murmushi ko su gaisar da ita sakamakon shirin da ta yi wanda ke nuna ko ita wacece take dan kallo ta amsa su da dan yatsina baki ko ta dan dauke kanta Baiwar dake biye da ita ke dan sake gyara alkhyabarta har suka karasa daga ciki wajen VIP plc ta zauna a wajen da yake nata ne domin shine numberta ta karra gyara zamanta tana maganar karshe da kawarta wace suka yi zasu hade a cen su yi wani program dinsu na harkar auren kawar tata A hankali ta girgiza kanta a lokacin da baiwar ta karra tambayarta ko akoy bukatar wani abin? Juyawa baiwar ta yi ta koma nata wajen cen cikin jirgin cikin jama'a tana sauke ajiyar zuciya da tunanin ta shiga ukunta da akace ta yiwa BAHIJA rakiya, ta tabbata tana ji tana ganni zata shiga garin manzo ta fito ba tare da ta yi sallah ba, watau ba tare da ta je masalaci ba, dan kuwa Bahija kashinta ne kawai ba'a wanke mata, yadda take zuba mulki a rayuwa ko ubanta bai kaita ba! A hankali ta dan karra gyara zamanta tana daura belt, sai kuma ta shiga dan duban gefe da gefenta dan gannin su wanenen Elhazan da duka hau VIP a wannan tafiyar? Na farko da ta fara kallo sai da ta kureshi da ido, domin sam bai mata kama da wani hamshaki ba, sai kuma ta tabe baki ta juya hannunta na dama daga wancen bangaren Ido ta zubawa wanda ke zaune a nan, cikin shiga yake ta simple doguwar riga fara kal kal kal , kansa baya dauke da hirami ko hula hakan ya bayanar da lalausan gashin kansa, hannayen doguwar rigar kuwa har kusan tsintsiyar hannunsa daidai da agogon da sai da ta karra zuba mata ido domin ko a ido ka kalleta ka san ba ta yara kannana bace, watau ba ta mun taso nace, ta ginanu ce har zuwa dan madaidaicin Alkur'anin dake hannunsa Wani irin yarrrrr tsigar jikinta ta bada, a hankali ta dan cire dubanta , sai dai tana juyar da kan nata ta sake juyowa ta kuma zuba masa ido, gashin kansa zuwa na girrarsa da na idannuwansa da dogon hancinsa da bakinsa sun fi komai daukan hankalinta A hankali ta dora hannunta daidai zuciyarta tana jin yadda take wani irin buga mata Da sauri ta rintse idannuwanta tana jin tamkar zata summa dan wani irin yannayi mai karfi dake sake ziyartarta........ 'Ya salam, wannan wanene a cikin garin AGADAZ? bako ne ko dan gari? Wani yare ne? Daga ina ya fito? Hasbunnalah..........' shine abinda take ta ayannawa a cen kasan zuciyarta, har aka gama maganar a daura belt da sauransu suka daga hankalinsa a kan Alkur'aninsa, ita kuma hankalinta a kansa......ta kasa gaskata irin dokawar da zuciyarta ke yi a kan wannan bawan Allah............ Ta yarda yau ta hadu da wanda yake daidai da ita .....A hankali ta dan sake gyara hijabinta da kuma alkyabarta ta yi dab gyaran murya dan baban burinta shine wannan bawan Allah ya dago idannuwansa su yi ido hudu da junna, sai dai kashhh har sadaden barcin dake surarta idan tana cikin tafia ya saceta bai dago din ba, Sai da ya kai karshen karatun da yake yi a hankali ya rufe Alkuranin ya rike shu a hannunsa ya kai dubansa kan Amintacensa yana dan masa alamu da agogo dan son sannin lokaci duda ta hannunsa dake sarkafe ama bai duba ba Lokacin ya sanar masa yana mai girmamashi sannan ya sake aunawa idan har sun yi tafia mai kyau nan da awa biyu sunna iya sauka domin sun yi tafiyar da dan yawa Sake komawa ya yi ya gyara zamansa ya 'unshe idannuwansa yana tunna Auta, ko yaya juwar? Ko ta saketa? In sha Allah idan ya dawo zai gayato mijinta ya zo su wuni tare ko zata ji dadin hakan, shi baya so ne idan ya zo din nan ta ringa kukan sai ta bishi, bayan a yanzu shi babu inda zai iya barinta ta je nesa da shi, sai ya gamsu da yannayin lafiyarta, ga Umma a kusa tana hakuri da ita sosai tana kula da ita, bata yadda amana ba, bata yadda zumunci ba, ya tabata wata rana Auta zata dawo normal irin na kowace mace Dan murmushi ya yi, idan har ta dawo haka, yaya zai yi da farin ciki? Ya Allah ya nuna masa *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣7️⃣ Dan murmushi ya yi, idan har ta samu lafia ina zai saka ransa dan murna?, Ya Allah ka nuna min.....ya yi wannan addu'a a kasan zuciyarsa Lafiya suka sauka a baban Birnin MADINA garin Manzo Tsakanin aéroport din da Hotel din da suka dauka da dan tafia, kasancewar ga gajiyar jiya, ga ta yau sai suka shige taxi su hudu suka nufi BABAN hotel din NOZOL ROYAL dake Abi Obaida ibn al jazrah street A hanzarce take, karra kallon motar dake gabansu biyu take wace ke dauke da mutumen da kuma jama'arsa, Adu'a take yi a zuciyarta Allah ya sa kar Motocin su bace masu, haka kuma ji take yi tamkar ta kwace motar ta tuka da kanta ko zata samu ta sada kanta a Hotel din nan Sunna karasowa shi fita ya yi ya yi gaba, Mutanensa suka tsaya biyan kudin, a lokacin ne itama ta fito tana mikawa Baiwar jakarta ta ce" Biya shi" da sauri ta shiga bin bayan wannan bawan Allah Kasancewar tun daga mettre dari ake tarboka dan a sadaka da dukkan abinda ya dace a wannan Hotel idan ka sauka a cikinta ya saka bai tsaya tsaye tsaye ba ya dan zanta kadan da balaraben dake yi masa magana cikin yaren larabci yana mai tambayarsa sunnansa da kuma number dakin fa akace masa an cirar masa Dan tsai ya yi ya dan shafa gaban goshinsa kafan dan shi kam bai san number dakin ba tunda ba shi ya cira ba gaskiya, Dan waigawa ya yi dan gannin ko sun zo, sai ya ga ta juya da dauri daga kallonsan da take yi Murmushin takaici ya yi yana basarwa, ya tabata bata gane shi ba, tun a cikin jirgi yake mamakin irin yadda ta lakanci kallo kamar wata bagidajiya, sannan da ya ga tana yawan kallon mutanensa ya zata ko ta ganne su ne? Shi dama gaskiya ba zata gane shi ba, dan ba wannan damar, idan ba na gi da gi dinsa ba ba wai lalle ka ringa ganninsa ba rawani ba, shima a lokacin da ta cika kallonsan nan gaba daya ya ringa ji a jikinsa an kura masa ido, da farko yaronsa ya duba ya zata ko shine ke masa kallon nan dan ya ji dalili? Sai ya gane ba su bane, asalima suma sun dan damu da yannayin kallon nata, sai ya basar ya ci gaba da karatunsa sai da ta yi barcin nan ne ya dan dubeta , kamanin mahaifinta ya fara ganni sai kuma suka karra tabatar masa itace yar gidan Bafansa ce A tausashe ya ce"ها هو الشخص الذي أخذ هذه الغرفة من أجلنا" ( ga wanda ya kama mana dakin nan zuwa) Ido ta zarro, a zuciyarta ta ayana 'Ya salam, balarabe ne ashe? Wayo Allahna, Ya Allah ka bani ikon tunkararsa ' Da sauri suka karaso ya fadi dakunnan, hakan ya sa akai masu jagora Idannuwanta sun gama rufewa, neman binsu take yi a lokacin ne mace yar uwarta cikin shiga harda nikaf da safar hannun ta tareta tana mai yi mata salama da fara kwatanta mata da tambayarta bata basu dakin da ta dauka ba kuma tana neman shiga lft Ido ta ringa zarrowa, hankalinta na neman tashi Ta san a nan kasar da ta sauko darajarta daya da baiwarta Babu wanda zata yiwa tinkaho ko isa, hasalima ba kowani balarabe yale mu'amalantar bak'ar fata da mu'amala mai kyau ba, duda ita din fara ce kal , ama kuma bakinta baya dauke da larabcin da matar nan ta yi mata A hankali ta ce" S'il vous plaît pouvez vous m'expliquer en français ? Je ne comprends pas très bien l'arabe " ( Dan Allah ko zaki kwatanta min da french, domin bana fahimtar larabci da kyau) Matar ta dan yatsina fuska ta juya ta koma ta fada a cen cewa matar cen freinch kawai take ji, dan haka aka turo mata wanda ke jin freinch A nan ya fada mata komai cikin nutsuwa A sanyaye ta ce" Kennan idan har mutun mai dauki daki tun daga gidansa ba, ba zai iya samu ba?" A tausashe ya ce" Gaskiya da wahala, ama bara na tambaya idan har akoy dakin da ba'a kama ba sai ki kama" Tana tsaye ana ta aiki da computer, kwararun ma'aikatan sunna ta aikinsu Wata mata da ta kama wani daki ta ce kawarta ta kamama suka sake tabowa, nan ta sheda masu kawar tata tace bata san dakin a wani hotel bravia zata sauka, dan haka sai suka cenza sunnan suka bata dakin sunna yi mata bayani kamar haka" Zaki ji dadin Hotel Nozol royal, domin a wannan waje akoy tsafta, akoy restaurant, sannan tsakaninta da kofar baban masalaci Al-masjid al nabawi tafia ce ta yan mintuna 10, kana yi kana hailala, sunnada gadaje uku, baban gado na Queen royal, da gadaje biyu, sunnada bayi tankameme guda mai dauke da jakuzi, ruwa na shower, WC, da kuma Buta ta karfe, a kulun za'a cenza maka abin shinfida da na rufa koda baka kwonta a sama ba, sunnada kur'anai da abubuwan sallah, idan budurwa ce ke bakida damar kawo maza wajenki, idan matar aure ce ke wanda yake da damar shiga wajenki mijinki ne,kina iya shiga dakin motsa jiki na mata, sannan akoy parking space idan kina iya hayar motar da za'a yi yawo da ke domin bakuwa kike ba zaki yi tuki da kanki a Madina ba, bakida takardar yar kasa, kudin parking din du minti talatin sarl biyar ne ba tsada........." Ita kam dakin ta shige tana kallonsa ta ce" Na gode" Kai ya gyada ya yi baya dan ya kula ta gaji ya fice Da sauri ta cire Alkyabarta da abin wuyanta ta ajiye a nan ta ringa kai kawo farcenta daya a cikin bakinta kanta tamkar zai tarwatse da tunani A hankali baiwarta ta dan duka ta ce" Allah ya karra maki lafiya, me kike da muradi kafin ki shiga wanka? Sai kin shiga kin fito zaki ci abinci ko kafin ki shiga za......" "Dan Allah ki barni da maganar abinci da dukkan abinda ya shafe shi, ba kin ga mutumen da muka taho tare ba, ga wannan kudin ki rike idan kin ji yinwa ki nemi abinci ki ci, ki sauka ki samo min wani daki yake, kar ki dawo sai kim samo min kin ji abinda na fada!" Jiki a sanyaye ta amshi kudin, zuciyarta na bugawa Wai mutumen da suka biyo wanda ke tare da baban bawan garin AGADAZ? To ita bata ji numbobin dakunnan da suka dauka bane? Ko kuwa? Har ta juya zata fita sai kuma ta dawo ta sake zubewa a kasa ta sheda mata ai gafa numbobinsu na dakunnansu Wani irin ajiyar zuciya ta sauke tana jin wani sanyi mai dadi na ratsata Har ta daga kafarta zata fice, sai kuma ta ja tana kallon jikinta Muryarta har rawa take ta ce" Ki bude akwatina ki ciro min abayata wace ta fi kyau, ki fitar da turare ki yi mata wanka sannan ki shigo bayi ki cudan bayana....." Haka kawai ta ga ya dace ta dauki wankan da ya dace dan ta leka bawan Allahn cen, ya Allah bata taba jin namiji ya shiga zuciyarta irin na yau ba, ji take kamar zata summa, gaba daya ta manta tabo kawar tata da tace ta sanar mata Hotel din da ta sauka dan tace mata ko ta kama mata daki a Hotel din da suka sauka da mahaifiyarta ko me? Ita kuma ta kiya domin ba zata so ta shiga dakin yaku bayi ba gaskiya, ta so ta je Hotel din da suke sauka sai gata a nan, duda kudin dakin ya bata mamaki tsadarsa haka ta dauki adadin kwanakin da take so ta saka masu kudin.....bata tunanin zata iya barin wancen gayen a yau Bayan ta shige ne aka sake kira, kawar tata ce, a dole baiwarta ta daga dan idan bata daga din ba tana iya jawa kanta matsala Da girmamawa ta sheda mata cewa ai a Hotel Nozol royal ne suka sauka Da mamaki kawar tata ta ce" A wani daki? Nima a nan din nake ai, nan din ne na kama mata ta saka na yi annuler, gani nan zuwa!" Wannan kennan ______________________________________ Hasken farin watan na yau ya masifar haska lungu fa sako na kauyen LABA Ga kuma fitilun aci balbal fa suka kunna harda gagan samarin da suke da Uba sanjo ya kasa watau wannan fitila mai shegen hasken tsiya sun kunna sun dage kafa sunna kallon yan matansu na wake ana shewa da tafawa abin gwanin birgewa Aminu ne ya yi murmushi yana kallon NADIRAH ya ce" Ta Aminu kin tabata yau zaki yi rawa a dandalin nan? Ta Aminu a kanki in ba sai na yi karin hamsin ba ubana goma!" Fari ta yi da idannuwanta ta kara gyara tsayuwarta ta ce" Aminun Indirah, sha kuruminla ka huta, mu bakwai ne zamu shiga ai yanzu yanzu, dan haka gyara aljihunka, ka dan dai ido a kanmu gaskiya yau ka saki kudi ka ji Aminuna?" Wani irin murmushi ya yi ya cira kai ya ce" Barama ki ga na karo a wajen Mutaha" Da ido ta rakashi har ya bacewa ganninta, haka kawai ta samu kanta da sakin yar dariya har tana rufe bakinta a lokacin da ya bacewa ganninta Yar dubu da ta dawo dan kamota su je su shige rawar ta tsaya kallonta ta ce" Dariyar me kike yi haka ke kuwa?" Murmushi ta yi tana sake dora daurin zanninta a saman rigarta mai hoto ta ce" Wai ki ji fa Hindu cewa ta yi walahi ifan Aminu na tafia kamar wuyan rakumin jeji, shine yau na ga ya yi gaba wuyan ashe zolo zolo yake biyarsa......" Ta karashe tana sake fashewa fa dariya dan har ga Allah abin ya shamaceta, kai Innarta? Innarta sai ta kasheta wata rana, Itama dariyar take yi ta girgiza kai ta ce" Ai kuwa ke kin san du kauyen nan babu ya Aminunki a gayu, zo muje dan Allah daga lamratu fa sai ni sai ke a wale, yau Adamu ya zo kallo Allah ya sa ya dubeni" Binta ta yi suka shige layin yan matan dake wake, kowace idan ta shigo da kalar bajintarta take kada abinda ta san tanada shi ta wake samrayinta ta koma, idan da yan cenjinsa tsaf ,ai shigo ya zuba mata su, idan babu kuwa abinda yake da shi zai yiwa makadin kyauta da shi Murmushi take yi a lokacin da Yar dubu ta yi wakenta tana kallon wajen Adamu, ama sam sai ya ki shigowa ya mata kari, karshema hala ta kusan gamawa ba'a yi mata ba Tana rangaji ta je ta dauko Uba sanjon Aminu hankali kwonce ta kai gaban makadi ta ajiye ta rada masa magana kamar haka" Na yiwa kawata kari da Uba sanjon nan, in da budurwar da ta isa ta tarbi uba sanjon saurayinta ta dauka ta yi kari da ita bismillah, Aminu ya saka min albarka, kuma zan yi rawa da kalabina a saman kaina idan ya fadi na yi alkawarin yiwa Aminu gabar kwana biyu!" Ihu aka dauka, makadin nan har saba babar rigarsa yake ya mike ya biyo bayanta ya sanar da danarwarta sannan ya gyara yar gagarsa ta kofi ya shiga kada mata Sai da ta yi gamo da fan kwalinta ta dora saman kanta sannan ta gyara tsayuwarta cike da bege ta shiga rerawa Aminu waka , ga fitinaniyar rawar da HINDU ta koya mata, wai rawar daka, jama'a rawa ce tamkar babu yayan hanji a cikin mutun, rawa ce tamkar kugu zai tsinke ana wani irin abu kamar babu komai sai duwawun, watau rawa dai irin ta SHAKIRA Har zanzana Aminu yake yi a lokacin da ya shige filin nan ya ringa mana mata yan goma goma a goshi yana bubudewa A kadan sai da ya zuba mata sitin da biyar ya laluba ya laluba sai kudin innarsa da ta aike shi kaiwa na dashi Wani irin zigashi da ake yi a yau ko mai gari ya ji sai gabansa ya fadi, shi ya san a kan NADIRAH ya shiga gaban maza, dan haka ya zarro kudin zubin dashin Innarsa ba tare da tunanin komai ba ya kalli makadi, makadi ya kalle shi ya shiga zarra yana zuba masa jiki har rawa yake NADIRAH ta fara zarro ido tana kallonsa, hakama jama'ar gari, ihu fa waje ya zagaye kira ake Aminun Indirah wuta Aminu wuta aminu, Aminu na wuta ba ji ba ganni Kanwarsa ta juya ta dankara a guje ta nufi gidansu har taka karangiya take yi, ama bata damu ba, baban burinta ta kaiwa Innarsu labarin cewa lokaci ya yi da zasu kai bayin Allan cen baban birni a masu tsakani, ga danta cen ya haukace ko kudin teburin nasa ya amsa yau yake bayarwa ko yayane? Abu dai ya giga Aminu ya bale ☹️☹️☹️☹️ Aminu ya balle jama'a mun shiga uku, Nadirah mata saman kanki ga inna nan tafe🤣😁😁😁 Cmmnt, sabon posting 😁 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣8️⃣ Raf Nadirah ta yi da hannunsa a lokacin da ya sake nufar aljihunsa ta tsayar da rawar tana kallonsa ta ce" Kai Aminu kudin nan fa? Ko kijmashin ka fara?" Sai a lokacin Aminu ya tino a cikin wani kudi ne yake baje kolinsa Idannuwa ya zarro ya kalli makadi, makadi ya kalle shi Gabansa sai da ya karra kwonci kwonci ya rufto, sai dai lokaci daya ya ji wani karfi ya zo masa a lokacin da amininsa Adamu ya dafa kafadarsa ya ce" Kai daya kake tal gaya na Indirah ikon Allah, kai ja mata ja mai dogon hanci kaine zaka haifowa dan mai gari mata gaba gaba kauyen LABA tafin hannunka mutumena, dole ka yi jarumin gwarzon kauyen LABA kai daya gaya, ko jaka dari ka zuba a rawar nan ta yi elhajina, idan baka daka da karfi ba watarana a gaban idannuwanka za'a cireta, nake fada maka Indirah ba karamar kadarah bace tanadinta mayar da kudi gida ne" Daria ya yi yana gyada kansa ya kalleta ya ce" Saki aljihun mana Indin Aminu?" Nadirah ta girgiza kanta ta ce" Wasa kake Aminu, kudin wa ka samu kake bararwa haka? Kardai na shago ne kake yiwa barin mahaukaciyar nan?" Kamata Yar dubu ta yi ta jata tana fadin" ke zo mu tafi, mu je mu je ga cen su hansatu sun kaure da fadan karin da Aminu ya yi, wai Hansatu ce take fadin a da fa Aminu ita ya so? Mu za'a kawowa bidi'a? Sun ha Aminu ya yi kudi za'a fara kawo masa hari ko? Aminu na INDIRAHn Yar dubu ne ba wata shegiya walahi!" Sakinsa ta yi tana kunce dan kwalinta ta ci damara ta ce" Ta samu , mu je, yo a kan Aminu in dan ni a kwana ana tseren rai a garin nan, sai gobe masoyi....." Daga nan wajen fadan nan suka je aka casu da su, Yar dubu kam ta jigata, ita kuwa ta sha dukewa domin ba zata yarda a lalata mata fuska ba gaskiya, da kyar suka raba kansu da kansu suka raka kuma tare ana tafe ana zaurance da yade yaden magana har kowace ta karasa gidansu ta shige *Safiya maraicen kura in ji yan magana* Bankadowar kofar gidansu ya sakata sakin tulun da ta nada gamo ta dora a kanta dan ta je ta dibowa Innarta ruwa a rafi Butar da HINDU ke kuskurar baki ta ajiye tana tafa hannayenta ta ce" Zan ga annabi idan na yi hali na gari, yanzu Indirar inna ba zaki daina kashe min tulu ba? Kin san tulun nan mu uku muka yi jayaya a kansa dan yanada saurin sanyaya ruwa? Kin fashe shi Indirah saura wancen na babanki shima ki dan dauko ki maka a kasa sai mu huta!" NADIRAH ta hadiyi yawu tana dake kasa kunne tana jiyo muryar innar Aminu a kofar gidansu Dam dam ta karaso ta rage murya ta ce" INNATA kamar muryar Inna Aminu fa, bakya ji tana fadin idan bai shigo ba zata muka masa faskare?" Kaffafuwanta ta janyo da kyau ta yi zaman yan makaranta tana kallon NADIRAH da sin karrin bayani, me kuma zai kawo innar Aminunta a karro na biyu gidan nan? Mema ta aikata to? "Allah jikanmu!" Innar aminu ta fada a takaice ta daka hannunta ta tankado keyar Aminu ya yi taga taga ya dake dukawa kansa a kasa , kana kallon gefen fuskarsa ka san ya maru bawan Allah Ido Hindu ta zarro ta zabura ta mike tana fadin" Ke bani hijabi ashe siriki ne da asusuba ko hantsi bai fito ba da Innarsa, Allah ya sa alkhairin da ya saba zuwar mana da sanyin safiya ne ya zo mana yauma" Rai bace innar Aminu ta ce" Zaki fadi haka, zaki fada haka uwar yan cin amana da cin zali, to bara ki ji Hindu ni nan innar Aminu a kan wannan mai ido ya na mayun sai na tsine masa albarka, ace na bi kasuwani, na sha zafin rana, na yi dakan fura na samo kudina na dashe ya je ya zubawa wannan la'ananiyar? Ni kuwa ai aure da Aminuna da wannan y'a sai dai idan kasa ta birni idona, kai dan Ubanka ka amso min sauran cenjin a wajenta ko sai na jibga maka faskaran nan ka summe kowama ya huta?....." Ta karashe da tartsatsin ihun da ya saka Aminu sake sinne kai NADIRAH hankalinta ya sake tashi, ta karaso ta duka tana kallon Innarta da ta ja tana kallon ikon Allah, a rikice ta ce" Inna kar ki tsine mana kin ji? Nawa ne kudin sai na saka Abana ya bani na kawo maki idan ya dawo daga birni, sababima zai bamu, ama inna ku daina shiga soyayarmu ni da Aminuna dan Allah, ni bai bani ko taro ba ki tambayeshi, ki daina dukansa kin ga fa ya yi uwa igiyar leko a ruwa" Ai kuwa innarsa ta sake kifa masa mari tana hankade NADIRAH da gangan domin dama damar nan take nema A zabure innar NADIRAH ta karaso ta saka hannunta ta hankade Innar Aminu sannan ta shaki kwalarta ta daga hannu zata rufta mata mari ihun NADIRAH da Aminu ya sakata dakatawa Da ihu NADIRAH tana dira ta ce" Innata aa aa maman Aminu ce" Shima a haukace ya ce" Inna kar ki yi mari ta hannani aurenta na bi duniya kar ki yi" Lebenta ta dantse ta daki kwalar innar tasa ta shige uwar dakanta Cen kasan gadonta na karaga ta lalubo asusun mijinta ta zauna ta fasashi ta shiga irga kudin dake ciki Biyu ta raba ta fito da shi ta mikawa Innar Aminu tana kallonta ta ce" Asabe, ki ji tsoron Allah, ki ji tsoron Allah asabe, ki sanni Allah ya yi hanni da zurfafa soyaya ko kiyaya, sannan ya ce idan zaka yi soyaya ka yi dominsa, haka idan zaka ki bawansa ka ki shi dominsa, kar ki kasance mutun mai fitina da rashin son zaman lafiya, ki sani nima uwa ce, kuma yarnan da gatanta, ba shegiya bace, ba maya bace, ba barauniya bace, ba yar iska bace, dan rashin son gaskiya danki fa ya yi likin nan ba wuka ta saka masa a wuya ya yi ba, a duniya menene maza basa yiwa mata?, Na karashe maki magana ni nan na hanneta amsar sisin Aminu, ko rake bai taba siya mata ba, bata amsa , bata so , nace ta bari idan ita din matar aminu ce a gidansa ya ciyar da ita, bana neman kai da yarinyar nan, ban kasa rike abina ba, ki sani du abinda kike yi da amsu ziga ki ba masoyanki bane, domin baki tsaya a kan huja kakarfa ba sai wata bankadafiyar hujarki marr ma'ana, kin dage dan yarinyar nan ta cika kyau ko me? Shin ita ta halici kanta, idan zaki iya ki iya da danki ki hannashi shiga sabgarta, ni kuma na rantse da girman Allah daga lokacin da Aminu ya nuna baya ra'ayin indi ta fita a harkarsa kennan dan ki bar ganninta haka na isa da ita!, Sannan ke kin san daraja kike ci, kina min takakiya ki ci min mutunci har gidana ni ta sarkin makada ko?, Ba damuwa, idan har kika kaini bango nice zan tarda ke!, Ke kin san wacece ni, ina daga kafa dan na ga yara sun dage, aure kuwa ba'a yi masa haka, to bari ki ji na gama maki magana idan Indi matar Aminu ce kina raye ko kina cikin ƙasa za'a yi a gama kina kallon yan dugwui dugwui a gabanki, idan kuwa ba matarsa bace du tsiya sai dai kowa ya yi hakuri, dan Allah kina abu kamar jahila, ki fice a gidan nan in ba haka ba, in ban cuje maki dan kwali na danna kanki a cikin ta murhun cen ba ni bace HINDU bace!" Gannin yadda Hindu ta farra hawa sama tana zarro mata ido tana neman dungure mata kai ya saka ta sake tatara kudaden da take jinsu da yawan gaske kamar sun fi natanma yawa ta karasa inda suke tsugune ta damki hannunsa ta ce" Tashi mu je, yau yau yau zan ga ubanka mu tsayar da magana daya fa yarinyar gidan rabe, yarinya na sonka kana janta a kas, tashi mu je" Kamar jansa take, a kan kaffafuwansa yake tafiya ama kuma kamar jansa take ya bita suka fice a gidan Hindu dake tsaye kallon NADIRAH take yi tana jira ta ga ta zabura ta bi su, sai ta ga ta share hawayenta ta mike ta dawo kusanta ta tsaya tana kallonta, sai kuma ta fada jikinta ta saki kuka mai tsuma zuciya tana cusa kanta cikin kirjinta Idannuwanta ta lumshe itama hawayen nata suka samu digowa daga gurbin idannuwanta, ta dagota tana kallonta ta ce" Kulan ya tafi ne ko? Kukan abinda mamansa tace kike yi ko? Yi hakuri yar albarkana kin ji? Yi hakuri ki daina kukan nan, na sha fada maki ki barsu du abinsu abinda Allah ya hukunta fa zamu gani a rayuwarmu kin ji?" NADIRAH ta ja hanci tana fadin" Ni yanzu na fara tsoron matar nan, ginnin da yake yi dakina da nata a hade suke, idan har ya gama ya tabata a gidanta zamu zauna makotaka, anya zata barni na rayu a gidan mijina? Imnata ko kaini zaki yi a bibila min fuskata na zama mai munin da take so? Ita in ba abinta ba ai nima ba wani kyan ne da ni ba tunda banida tsayi ko Innata , kuma na ji ana cewa mace idan ba tsayi batada wani kyau ko Inna?, Dan Allah ki kaini a bilen fuskata" Janta ta yi suka karasa wajen zamansu domin rana bata fito ba bale su je kasan shuka suka zauna A sanyaye ta ce" Kin san na tabata wata rana Innar Aminu sai ta kaunace ki, Allah zai saka mata kaunarki tunda batada dalilin tsanarki, kuma ba za'a maki bile bile a fuska ba, babu kyau fa a lahira da wutar jahannama za'a gogewa masu shi, ke nu kam banma ga abin daga hankali ba Indirahna, ki kwontar da hankalinki, idan kuwa zaki bini birni satin nan mai kamawa sai mu leka mamanki mu gaisar da ita sannan mu wuce gidan kallo mu yi kallo sai mu karkato kasuwa mu dayi kayan yan gayu harda takalmi kin ji?" Kai ta gyada tanna murmushi ta ce" Inna hala asusun da zaki siya min gadon mai runfa ne kika fasa? Ko na Abana ne da yace zai min gara buhu takwas?" Yar dariya ta yi ta ce" ina ai asusun gadonki ba za'a fasa shi ba ko ana ha maza ha mata, na abankine, barama na kimtsa tarbansa dan na san yana iya kirtan ba dadi dan na taba asusun nan na gararki, zo tsefen kaina na yi sheme sheme a tsakar gidan nan ya tardomu a haka sai ace innar Aminu ta shinfideni, na tanata ba zai ji haushin kudinsa da yawa ba" Dariya ta yi ta kwontar da kanta a saman kafar Innarta, a hankali ta ce" Innata, ina yin adu'ar nan fa, ko yau da kika tadani sallar asuba da na yi raka'atanul fajr kafin a yi kiran sallar asubah na fara salatin nan, da aka yi sallar aka gama na dora na yi ta yi , na yi ta yi sai da na kai dubun nan, sannan na dora fa adu'o'in tsarin da Innar birni ke koya min, na yi azhkar sannan na roki Allah ta bani miji na gari Aminuna......." Murmushi Innar ta yi tana shafa kanta a hankali ta ce" Ki ci gaba da yi, ki yi ta yi, kin ga ni yanzu idan ban yi dubun nan kafin na kwonta ba bana iya barci, komai gajiya sai ki ga ina zabura, kuma adu'o'in neman tsari sunne makamin mumuni, babu boka ko malamin da ya fi bakinka da na iyayenka, ka fadawa Allah da kanka, to fa in du duniya zata tsaneka Allah na tare da kai, wani lokacin zaka ga kana ta Adu'ar kana ta yi biyan bukatar bai zo ba, to ka sani alkhairin ne a wani bangaren wanda Allah zai tabatar maka, kai da kanka sai ka yi mamaki, yanzu dai ai ba'a kai rikici irin na makada ba, ama ki duba ki ga Abanki kulun yana sama, makadi ne ama a haka yake neman kariya a wajen ubangijinsa, ki ci gaba da neman zabin Allah, ama ki daina cewa alkhairi Aminu dan baki san wannan mai wuyan uwa marikin lema bane alkhairin ko mai garin nan bane" Kai ta dago da sauri tana cuno baki ta mike tana fadin" Kai inna, ke dai ba za'a yi hira ta zaman lafiya ba sai kin kawo masu mulkin nan da basuda tunanin komai a rayuwa sai mulki, ni fa ko sarkin yan tasha bana so walahi in dai sarki ne!" Da ido ta rakata domin ta warci dayan tulun fa ya rage da garaje ta yi gaba Ajiyar zuciya ta dauke ta ce" Tuluna, Allah ya sa ka dawo da ranka kar wani ya tabata ta mula masa, ni kam ban san a ina Indirah ta gaji fada ba sam" ( to fah😁😁😁) _________________________________ Shayin da ta kurba a bakinta mai dumi da dandanon zuma kamar zata yi tagia ta furzo a zabure tana sakin kofin kwalbar mai dauke da ruwan shayin ya bare a saman cinyarta A haukace ta saka ihu tana fadin" FADIME FADIME, shigo shigo bani ruwa da gishiri ciki na kone kafata" A hanzarce ta shigo ta yi kicin kanta a kasa domin Mai martaba na zaune ba zaka yi kallo irin na kure waje ba dan gudun yin laifi wajen matarsa mai haukatacen kishi Da sauri ta dawo kanta a kasa domin kunyar lamarin take ji a zuciyarta ta fan zuba mata ruwan a saman cinyarta da ta kwaye gaba daya kamar wata wace ta soye wannan tona sirrin jiki haka "Duba min da kyau na kone ko?" Gimbiya ta fada tana rinrintse ido A hankali ta duduba wajen, ya dan yi ja dai ama ba zai tashi ba tunda an zuba ruwa mai dauke da gishiri ai Kai ta girgiza da nutsatsiyar muryarta ta ce" In sha Allah ba zai tashi ba " Kai ta gyada tana cire dubanta a kanta ta mayar gefe tana saka yar yatsarta a bakinta ta dantse ranta a bace da maganar da mijinta ya zo mata da ita, ba dan komai ba sai dan tunaninta ai kashe mata ya kawai za'a yi, duda baban mutunci da daukaka ne zasu karkarowa kansu,ama kuma yarta fa? Da ido ya raka FADIME har ta bacewa ganninsa a hankali ya sake shafa gaban kirjinsa yana cire tunanin dake ransa ya sake fuskantarta ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 0️⃣9️⃣ Ya sake fuskantarta ya ce" Kina nufin maganar nan ce ta saka ki sakarwa jikinki shayi?" Juyowa ta yi, dan a lausashe ya yi maganar yanzu ta zuba masa ido Kai ya gyafa ya sake kausasa muryarsa yana kallonta ya ce" To ki kama kanki, ki tuna babu wanda ya sakani a wannan matsalar sai ke......, Bakida hurumi a wannan maganar, bakida abinda kika isa ki ce a wannan maganar sai fatan na shawo kan yata ta aminta da maganar nan, idan har kika kuskura kika yi wani abu na rantse maki sai kin kasa gane kanki bale har wani ya ganeki!" Da ido ta rakashi har ya ficewarsa Bayan fitarsama ta dauki minti biyu kafin take mikewa tsaye ta yi dakinta Wayarta ta lalubo ta zauna ta ci gaba da doka wayar sarauniyar dogon dutsi, sai dai amsar daya ce wayar bata shiga Wurgar da wayar ta yi ta doka hannunta a jikin abin gadon nan ranta bace ta ce" Ni zaka dauka , ka kaini gaban dan cikina ka gurfanar da ni, n bashi hakuri sannan na bashi yata kyauta? Yar da nake da burin a aurenta na tara dukiyar da ban taba tarawa ba a duniya? Yar daya mace kwalin kwal ka zo min da maganar wai idan ta shiga ba zata dauki lokaci ba zata zamto itace magajiyar garin Agadaz? Ta yaya? Ta ina? Lalle yau da na same ki a wayar nan sai na fara maki alkawarin idan har aka aurawa yata UMUGHLUK ITIFAL Walahi walahi sai na halaka ki da kaina kafin zakin sarakai ya kama ki,!" Ta idasa tana cure daurin dan kwalinta ta zauna ta shiga tunanin abinda ya dace da hanyar da ta dace ta bi dan magance wannan matsala, ta san waye mijinta, tanada iko a garinsa ama fa a wajen talakawa, bata isa da shi ba, abinda ta fi karfi kishiyoyinta ne, summa dan ta tara yaya da shi fiye da su, dan a cikinsu daya tak ce ta haihun itama shamatarta ta yi, ama idan abu ya hado su magana daya yake yi baya sake bi ta kai kuma ta zauna dar ba maganar dagawa ____________________________________ *Madina garin manzo, BAYAN WASU KWANAKI* "Ya salam ki daidaita numfashinki, dage nikaf din ki shaki numfashi haba BAHIJA!" Kawarta ta fada a dan rikice a lokacin da ta shiga wani irin numfarfashi sama sama tamkar zata sume Yadda tace din ta yi, watau ta dage nikaf dinta domin ba zata iya shakar iska da kyau a rufen nan ba, sannan ta mike ta dan yi gaba kadan ta lumshe idannuwanta har numfashinta ya daidaita sannan ta sake dawowa ta zauna ta sake zuba masa ido tamkar zata ciro idannuwan nata ta lika a fatar jikinsa A nutse yake tsaye ya basu baya, shigar dake jikinsa yau sak irin ta larabawa ce, wato ya daka alkyabar nan tasu mai ruwan yelow, ya dora hirami a saman shigarsa ya dan nade hiramin baya, haka kuma a tsayen da yake hannunsa daya a bayansa haka a jimke, dayan kuwa daga gaba sunna magana da wani mutumen da kana ganninsa ka san shima baba ne Kai ta dora saman table din cin abincin a hankali idannuwanta suka ciko da kwallah tana sake yi masa kallo wanda ya wuce misali A tausashe balaraben da suka yi aikin umurar tare ya sake dubanta duba daya tak ya dauke dubansa yana dan sake kallon restaurant din a ransa yana ayana shi yasa hotel din nan wani lokacin takeda matsala, domin akoy dan wajajen da ake hadewa mata da maza ba wajen ibada ba, hakan kuwa ba dadi, dan yanzu matan da mazan duka sai a hankali, Dogarinsa ne ya karaso ya yi masa bayani kasa kasa sosai, a kan maganar juyawarsu gida ne A tausashe ya ce" Aa, ka daukar mana na gobe idan da hali, garina na zuciyata, ga kuma Auta" Kai ya gyada ya juya cikin takun karfinsa, shima shigar larabawan ce a jikinsa abinsa Kujerun alfarmar dake ajiye suka karasa suka zauna, a nutse ya lankaya carbinsa a hannunsa ya sake duban Abu huzaifa ya ce" Sosai sunna saka abaya, zan iya ce maka a yanzu a garina Abaya da lafaya ta zama kayan ado a wajen yan mata da kuma matan aure, ai sunna son shiga irin ta larabawa" Kai ya gyada yana murmushi ya sake duban ASADEEK ya ce" Ka san me ya fi bani sha'awa da kai?, Irin yadda kake nema, kanada dama sosai, ama kuma kana nema sosai, babu ruwanla da kwonciya a nemo a kawo maka ka ci ka tada kai, idan dai zaka mayar da taro kadago baka tsoron hakan" Murmushin da ya yi a yanzu shi ya saka BAHIJA furta" Wayo Allahna, zan je, walahi yau zan je, zan tunkare shi" Kai kawarta ta girgiza tana dafe goshinta ta ce" Dama ki daina ba kanki wahala, irin larabawan cen ba zasu taba auren bak'ar fata ba, bayan wannan irin yafda kike tsoronshi ina tsoron ki zamto baiwarsa, ki duba ki gani sati biyu kennan ke ko masalaci baki je ba, tun baki san lokacin da yakan dan wulgawa ba har kika sani, sau nawa kina yinkurin hakan bakya iyawa, uwa uba kwaliyar yi kike yi ama kamar bai san da ke ba, ki yi hakuri kawai ki........." Ido ta zarro sanadiyar gannin Bahija ta mike ta nufi inda suke din Sai dai kafin ta karasa ta ga rusheshen bodyguard dinsa ya tsaya a gabanta fuskarsa ba alamun dariya a kausashe ya ce" Ina zaki je?" Gabanta banda dokawa babu abinda yake yi, hakan ya haifar mata da fitar hawaye tana shirin bashi amsa suka ji muryar Balaraben nan ya umarta kan a barta ta karaso Wata irin ajiyar zuciya ta sauke jikinta har rawa yake ta karasa wajen da suke zaune ta yi salama muryarta har tana rawa rawa Sannin mahinmancin salama ya saka shi amsawa a saman lebensa sannan ya dan juyo kadan ya sake kallonta ya kuma dauke kansa Tsaye take tana murzar hannunta har sai da balaraben ya ce " Bismillah mana yan mata?" Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta zauna a kujerar dake face da su gabanta na ci gaba da faduwa Rasawa ta yi, shin kuka zata fashe da shi ko kuma ta ci gaba da kokari har ta gama abinda ya kawota? Nikaf din ta sake dagewa dan ta tabata bai ga kyanta da kyau bane wannan mutumi A sanyaye ta ce" Dama , dama zuwa na yi, ina so na ganshi......" Inda ta nuna din ya kalla, sai kuma ya sake kallonta Dan murmushi ya yi ya furta" Bismillah" Sake kallon balaraben ta yi da kyai, gannin ba zai basu waje ba ya sakata sauke ajiyar zuciya, kirjinta na ci gaba da dokawa ta sake kallon bawan Allahn nan A hankali ta ce" Sunnana BAHIJA, ni yar sarkin garin Tanut ce, mun yi tafia tare har gashi za'a fara komawa, ban san shi ba, kuma ina son na sanshi..... Ina matukar son na san shi" Da mamaki balaraben nan ya kalli ASADEEK, wanda idannuwansa kawai ya lumshe yana mamakin lalle lamarinta ya girmama, al'amarinta ya giga, Dan sake kallonta ya yi, a sanninsa masarautar TANUT da ta AGADAZ masarauta ce ta familly daya? Bata sanshi bane ko menene? Da mamaki ya ce" Aa, baki gane shi bane? To ai.................." "Hhhhhhhhhhhummmmmmm, " ya yi gyaran muryar da ta saka su kallonsa gaba dayansu A hankali ya kalli wajen pepper da byro ya janyo su cikin nutsuwa ya rubuta mata numbarsa ta sirri ya mika mata ta hanyar ajiyewa a saman table din hankali ya sake kallonta da firgitatun idannuwansa sannan ya ce" Cl me." Wata irin ajiyar zuciya ta sauke hadi da sakin lalausan murmushi ta dauki takardar har kamar ta duka wajen godiya ta juya ta nufi wajen kawarta kamar zata kwaso shoki dan farin ciki Da mamaki ya kalli ASADEEK ya ce " Me kennan MAN?" ASADEEK ya dube shi, yana basarwa ya ce" A ina fa?" Murmushi ya yi shima yana girgiza kansa kawai ASADEEK kuwa ya dantse lebensa a kasan zuciyarsa ya ayana' Yaro man kaza.... Koda yake ba laifinki bane laifin zuciya ne' Daria ta fashe da ita tana sake rike takardar nan da hannayenta biyu biyu, ta kai daidai hanci ra ta sinsina tana lumshe idannuwanta sannan ta dauki jakarta a hannun baiwarta ta saka tana kallonta ta ce" ki rike takardar nan Mudin ranki kin ji?" Kai ta gyada da sauri tana rikewa da kyau din Da mamaki kawarta ta tafa mata ta ce" Lalle na yarda, kin kamu sai gyaran Allah, Amma kawata bakya tsoron wulakanci irin na Da namiji?, Kika yarda ya san kina sonsa bakya tsoron abinda ke iya haifarwa? Kin san fa maza bale masu kudin nan" Murmushi ta yi ta ce" Ai koda ya yi girmansa ne, kawata kin ji hannuna har yanzu kanshin turarensa yake?, Zan bi ku gida jibi dan burina na je na samu mama da wannan albishir, na tabata sai ta fi kowa farin ciki domin irin burin namijin da take min kennan" Haka suka ci gaba da hirarsu cikin sakewa, wani tsare tsaren da basu yi a kwanakin da suka shude bama sai yau suka yi shi a sake hankalinta kwonce, domin gani take yi tunda har ta damu number wayar mutumen cen, komai ya gama sai shafa fatiha, ta yi miji na kece raini, dan kwalisa mai kanshi. __________________________________ Yan umarah masu babar tafia watau VIP tuni jiragensu sun fara dawo da su gida Tun da safe suka karaso garin Niamey, daga nan luma suka nufi AGADAZ a wani jirgin, hakan ya sa tunda ya samu ya shige, sallah kawai le fitar da shi ta boyayiyar hanya har dare ya shigo ya kwonta dan samun hutu ko yayane, domin ya sani a gobe zai yi fitar wuri Fada dan gannin abinda ya faru bayan baya nan ____________________________________ Tarba ce akai mata wace ko mahaifin nata ya sameta ya more Yayunta biyu suka daukota daga filin jirgi, sai sangarta take zuba masu irin ta sangartatun yaya, ga baban farin cikinta fa murnarta shine ta karasa gida dan ta sanar da abinda ke zuciyarta wa mahaifanta Gaisar da ita ake yi, ama sam hankalinta ba a kan kowa yake ba, ga alkyabar da ta dora sai walwali take hakoran makarta na wal wal wal A nutse Mahaifinta ya mike ya tarbota a jikinsa yana murmushi ya dago fuskarta ya furta" Farin cikin Aba?" Murmushi ta saki ta karra dubansa ta ce" Abana" Mhaifiyarta ta karaso itama fuskarta dauke da fara'a tana kamota jikinta ta ce" Mu karasa ciki, wannan farin cikin fa?" Ajiyar zuciya ta sauke tana daga idannuwanta tana hangensa a idannuwanta a lokacin da zasu tafi jiya, kamar ta biyo su su dawo tare Har sun shige mahaifinta ya dan biyo bayansu yiwa mahaifiyarta maganar ya ce" ki tabatar kin shirya tafiyar nan, da sasafe zamu fita, sannan ki tabatar a yau ba sai goben ba kin fara yi mata maganar dan ta san da abinda ke jiranta" Jiki ba karfi ta gyada kanta ta shige cikin tana kallon yar tata da ta cire Alkyabarta ta kuma cire abayar dake kasa daga ita sai Pant da bra ta dauki tawul ta nada a kirjinta tana murmushi ta ce" Mama, tsaya na fito mamana, mamana akoy hira" Mahaifiyarta ta dan zarro ido ta ce" Ke baki gaji bane hala? Aikin umura ga kuma zaman jirgi gaki da son jiki?" Murmushi ta yi tana girgiza kanta ta ce" Mama, ba zaki gane ba, abinda nake tare da shi ya bige maganar gajiyata, mama bani minti daya" Da murmushi ta rakata sannan ta mike ta janyo abubuwan da aka zuba mata abinci ta shiga zubawa a cikin plate tana dan duba wayarta ..........MAMA........ Ta fada a hankali bayan ta zauna daf da ita A hankali ta dora kanta a gefen kafadunta ta ce" Bam taba tunanin a Africa, a karamin gari irin namu zan hadu da shi ba.......,ama na tabata zuwa ya yi, da ganninsa ba haifafen kasar nan bane........, Mama ban taba gannin tsarin halita, nutsuwa, kyau, aji da nutsatsen arziki irin nasa ba, shi din ba tara bane, goma ne..... Mama tunda na je ko zama ban samu ba kulun tunaninsa, har kuka na yi............ Mama na samo maki sirikinki, wanda kike min fatan samowa, mama zan faranta maki ranki, zaki yi yadda kuke so, farin cikinki zai zaga duniya, zaki kece raini......idan kika ganshi sai kin yi farin cikin da baki taba yi ba....., Baban burina shine ya amsaniya kuma yarda da ni"...... Ta karashe maganar tana dora kanta a kafadar mahaifiyarta, wace ta yi mutuwar zaune Hankalinta tashe ta dago fuskarta tana kallonta, a sanyaye ta ce" BAHIJA, maganarki ke kaini wani tunani daban, kamar wace ta fara soyaya?" BAHIJA ta yi murmushi har idannuwanta suka cika da kwallah ta gyada kanta a hankali ta ce" Mamah, soyaya kam na shigeta mai karfin gaske Mamah" Da sauri uwar ta mike tsaye tana sake fuskantarta Ajiyar zuciya ta sauke mai zafi da kunna tana kallonta Sai kuma ta dawo ta zauna bakin bed tana dauko yannayi na serius ta ce" Ki saurareni da kyau BAHIJA, kina jinna, ko me kika dauko daga tafiyarki li ajiye shi ki zubar ki fuskanceni da kyau, wannan magana da kika dauko sam ba zata yiwu ba, domin mahaifinki ya bada ke wa UMUGHLUK ITIFAL!, A gobe gobe zamu je maganar nan in sha Allah, idanma me kika dauko ki barshi domin lin san ba maganar wasa ko ta kawo wasa a ciki!" Wata irin zubowa kasa ta yi har tawul dinta na kwoncewa daga kirjinta yana neman faduwa Bata damu da riko shi ba, sai idannuwanta da ta fitar waje gaba daya , Da wata irin muryar kuka tana kallon mahaifiyarta ta ce" Mama? Ni? Wa zakin sarakai?, Mama ni? Mama yaya ina maki maganar namiji, namijin da na gano da idannuwana, wanda na kasa zuwa masalaci dan kar ya bace min, ke kuma kina min maganar wani wai shi zakin sarakai? Mutumen da babu wanda zai ce ga kamaninsa? Aba kulun yana kwatanta kamaninsa dan shi kadai ke ganninsa ba rawani, ko ke kin taba ganninsa ba rawani? Ta yiwu wani nakasashe yake, ko wani mai cutar hauka ne irin na kanwarsa? Wai mema ya kawo maganata ni da wani ZAKIN SARAKAI? Mama, ki cireni a ciki, bana gaba bana baya Mama, dan girman Allah ki ga abana ki sanar masa walahi walahi idan ya saki ya aurani wa ZAKIN SARAKAI komai na iya faruwa, ciki harda mutuwata, uwa uba harda tonuwar asirin mutuwar GWAG.................." HADIYE maganarta ta yi, sakamakon gigitacen bakon abin da ya ziyarci fuskarta, wanda bata taba ganni ko hasashensa ba, HANNU ne mai zafi fa kunna ya sauka a fuskar da hannu bai taba hawanta ba dai dan ya shafata ko ya yi mata kissssssss, A haukace uwar ta mike tsaye, jikinta na rawa tana kallon mai aikin nan A haukace Yar ta budi baki zata sake kurma wani ihun ya dake saka bayan hannu ya kai mata ............ Asalamu alaikum wa rahamatullah 🥰🥰🥰🥰 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 🔟 Wani bahagumen duka da bayan hannu ya sauke mata a gefen bakinta wanda ya sakata kusan summa a zaunen da take ta kwala wani ihun ta nemi jirkicewa kasa tana sakin tawul din gana dayansa, domin ji ta yi kamar ranta za'a raba da gangar jikinta Sake binta ya yi ya maka mata kafarsa ya sake dagawa zai kuma dima mata wani dukkan mahaifiyarta ta rukunkumeshi tana ihu da kuka tana sake rikeshi idannuwanta waje tana fadin" INNALILAHI WA INNA ILAIHI RAJUNE, KASHETA ZAKA YI? KASHETA ZAKA YI?" Jajayyen idannuwansa ya sauke a kanta, da karfi ya hankadeta itama gefe sannan ya nuno masu yatsarsa gaba dayansu muryarsa a kausashe ya ce" A kan mulkina, ina iya kashetan , ke koda ita daya na malaka idan har sakaken wawan bakikin mai jaza min masifa ya sake furta mata sirrina da hannuna zan shaketa sai na kasheta sannan na saketa!, Ke ba sakarya bace? Ke ba mahaukaciya bace? To ki sani wahalar sai dai ta kare a kanki, ba dai ni kadai ba, wato ke baki iyawa bakinki ko? Jira kike na zo na fada maki sirri ki bazani ko? Sai dai mu lalace baki dayanmu dan na rantse maki da Allah tare zamu rufta!, Kin sakata a gaba dama har na koma na dawo na san sakaran son da kike mata komai na iya faruwa, ki saurareni da kyau, walahi, walahi bilahilazi ki iya da ita, ki san yadda zaki yi da ita, a gobe gobe zamu sauka a garin AGADAZ mu kai maganar nan, kuma ta zaunu idan har kika yarda wani abin ya bilo daga ke har ita kunna jan numfashi ta bakinku kunna kallona sai na kashe ku!, Har kiyama zan aika ku!, Kin ji na rantse maki, sha sha sha, bakinta ya saki ya fadi wani abin....zaku kwashi kashinku a hannunku walahil azim!" Ga mamakinsu, ga baban mamakinsu, idannuwanta ta dago tarr ta saka dubanta a cikin na mahaifinta, duda idannuwanta sun rine sun yi wani irin ja sanadiyar marin da ta sha ta budi bakinta tana kallonsa ido cikin ido ta ce" ABA, kan nufin idan ban yarda aka aura min mutumen da ka fi tsana a duniya ba sai ka kasheni?" Babanta ya gyada kansa yana sake tabatar mata Wani irin murmushi ta yi mai tsauri ta taka tna daura tawul dinta ta nufi wajen bayi, sai da ta kama bayin ta rike kofar tana kallonsu ta ce" Lalle kuwa da ka jima baka kasheni ba, domin na rantse maka da Allah ba zan auri Sarki ba, bana cikin tsarin wahalarku ku duka, ba zaku sakani a ciki ba, idn kuwa ka nace ka aura min din ka gani, dukkan abinda kake tunanin ban sani ba na sani kuma ba uwata ta sanar min ba!, Kar ka manta da ni kake yawo?" Bam ta shige ta mako kofar tana dingishi Wani irin kukan kura ya yi ta karasa ya ringa jijiga kofar yana fadin ta bude masa,ama firrr ta ki budewar Juyowa wajen mamanta da ta yi mutuwr tsaye tana kallon taurin kan da yarsu ta yi irin na ubanta ya ce" Lalle yarki bata sanni ba, ama ina mai tabatar maki zata sanni kwana kusa in sha Allah, ki tabatar kin sameni a falona!" Fuuuuu ya juya ya bar dakin, ya fice yana sake kallon FADIME dake rabe cen kanta sade, da sauri ta daga kafarta dan ta bishi sai dai ganin kamar ya juyo yana kallon Fadime sai ta tsaya tana sake kallonsa Har ya wuce Fadime din ya dawo ya tsaya , a kausashe ya ce" Ina fata halinki na rashin saka kanki a inda bai shafeki ba yana nan?" A tsorace ta dago ta dan dube shi, sai kuma ta sake sada kanta tana gyada kanta Huci ya sauke ya juya ya wuce a falon gaba daya Ita kuwa Gimbiya dake tsaye tana kallon Fadime juyawa ta yi ta koma dakin wajen Bahija Bayi ta nemi zarcewa, sai dai abin mamaki sai ta ga Bahujar a saman gadonta a dukunkunne tana rawar sanyu Da sauri ta karasa saman gadon da Bahija take dukunkunne tana rawar dari ta hau ta kuma talabota tana kallonta a tsorace da halin da ta nuna ta ce" Bahija? Abanki yau kika kalla kika yiwa wannan furuci? Bahija Abanki?" Bahija ta dake fashewa da kula tana mayar da kanta saman cinyar uwar Mamanta ta ce" Bahija, ki yi shiru haka kin ji? Ki yi shiru Bahija kin fa san idan ran mahaifinki ya bace babu abinda baya fada, ransa ne kawai a bace kin ji? Ama kuma wannan abu da kika yi ya tsoratar da ni, Bahija abanki ne fa, kin fi kowa sannin irin soyayar da yake yi maki, dan yau ya nuna yana so ki masa wannan yar alfarma ta takaitacen lokaci dan kema ki karra samun kwonciyar hankali a rayuwa sai ki kiya? Ina cewa abin alfaharinki ne ko cikin kawayenki a ga waye mijinki, ina cewa sai kin fi kowa farin cikin wannan hadi fa Bahija?" Bahija ta dago rinanun idannuwanta tana kallon mamanta, a hankali ta budi bakinta muryarta a shake sosai ta ce " Mama, ransa a bace? Na masa alfarma? Kennan ni na kashe kaina ko? Ai alfarmar da zan masa shine na bijirewa auren nan, Mama ni fa ban damu ba, da gaske ko da wasa yake duka ba sunne a gabana ba, abinda na sani shine ba zan taba yarda da auren wani da ba wanda na gani a cikin jirgi muka yi hotel daya da shi ba, mama kina maganar kece raini, akoy wace zata fito da mijinta na fito da nawa a cikinsu ta isa daga kai? Mama kyan, ajin, kudin , hutun, tsarin, ilimin ya fi su walahi, Mama bara na karasa maki magana domin Allah, ni fa ba zan auri Sarki ba, ga wanda nake so zan nemo shi ko a ina yake, zan kuma kawo shi gidan nan a aura min, idan ba haka ba kafin ya kashenin sai na tona waye shi kuma na kashe kaina da kaina, ni fa a kan wannan mutumen ba mutuwar nake tsoro ba, tsoron rasa shi ya fi mutuwar karfi! Ba zaku fahimci me nake ji a zuciyata ba? Taba kirjina ki ji? Ko menene na hadu da shi mai zafi ne, kuma ina shirye da samama kaina shi ko ta aure ko ta wanin aure, ni dai sai na raba wannan mutun da kowa ya zama nawa ni kadai!" Tabas mahaifiyarta bata taba haduwa da tashin hankali irin na wannan rana ba, kanta ya coshe, ta rasa me zata tuna , ta rasa wani irin tunani ya dace ta yi, gaba daya hankalinta a tashe yake Da kyar ta ringa rarashin yar tana fada mata ta fauna maganar zata kashe kanta, mahaifintama ransa ne a bace, ita kuwa ta tsaya a kan bakanta bata da niyar ja baya, a kan mutumen da ta hadu da shi tana iya yin fito na fito da mahaifinta! UMUGHLUK ITIFAL kuwa su da shi, ba zata taba aurensa ba, ita inama zata iya zaman aure da mutumen da kowa ke tsoro, mahaifinta kansa tsoronsa yake yi kamar ya mutu, ama ita zai mikata ko? Aa walahi ta san ciwon kanta idan kowa bai san mata ba Da kyar ta rarasheta ta sha maganinta sannan ta rufo mata dakin t tafi da ky din da kanta dan ba zata bari ba aje ya dawo su halaka junna, tana so mijinta ya gane idan me y'arsa ta zama halinsa ne kuma shi ya kaita ya nuna mata, a yanzu bashida kaico walahi! Wajen fa FADIME ke zaune ta karasa ta tsaya rana karra kalle mata kallo Ta sani sarai, a duniya idna akoy matar da mijinta ke rakawa da ido wannan matar ce, ko me yake yi idan ta zo waje sai ya dakatar ya bita da ido, koda bai fada ba ita ta dade da sannin begen Fadime ya cika zuciyar mijinta, shi yasa take kafa kafa sam bata wasa da sakacin da zai saka UMUGHLUK ITIFAL jin labari ya kashe mata miji a kan baiwa! A kausashe ta ce" Kina iya tafiya " Ajiyar zuciya Fadime ta sauke ta mike tana sake dan dukawa ta ce" Allah ya tashe mu lafiya Ranki ya dade" Gimbiya ta tabe bakinta ta rakata da muguwar harara har ta fice tana tafiyarta cikin sanyin hali A nutse take tafia, duda dare ya yi ama da fitilu haka kuma da mutane dake yan shagulgulansu jifa jifa Tana karasowa bangarensu ta kunna tocila domin a nan din akoy duhu , haka kuma a zuciyarta sai Adu'ar tsari take yi Da sauri ta dakata da tafiyar a haskawar farko sakamakon kan fuskar mutun da ta haska Sai da ta sake haskawa ta zuba mata ido da mamaki muryarta kasa kasa ta ce" Kamar INDI?" NADIRAH ta turo baƙi tana sake shagwabe fuskarta sai soshe soshe rake yi Hindu ce ta fito tana fadin" Dan karbi wannan shafa mu gani? Haba tar autana ki bari mu musu kwana daya jal sai mu tafiyarmu kin ji?" Da takaici Fadime ta ja dan tsaki ta karasa tana janyo tabarmar kaba ta yada masu a nan tana amsa gaisuwar Hindu dake mata marhaba da gaisar da ita a mutunce tana murmushi Fadime ta ce" kun ci abinci kuwa?" Hindu ta ce" Aa so nake na lalabata, kin san ita daga mun sako kafarmu masarautar nan sai tace ita ranta baci yake, kaikayi masarauta ke sakata, ita ji take kamar ta je ta mari Gimbiya, shine nake mata yan turarw turare kar aje iskarsu ce bata hadu ba" Kwaryar da Inna ta dauko da ludayi dan dama masu furar da ta tarar mijinta ya kawo mai yawa ta dan dakata ta kalle su daga ita har innar tata Bata ce da su uffan ba ta cira kai ta karasa wajen tabarmar kaba ta budeta sosai, domin ita ta saka abinta da kanta fadadoya ce tabarmar ta cire hijabinta sai dan kwalin dake ciki ta yafa shi da kyau a kanta ta tankwashe kafafuwanta ta saka ludayin nan sannan ta shiga damawa HINDU ta turo baki tana sake kamo hannun yarta kasa kasa ta ce" Kin ga, ki rufa mana asiri mu yi kwana biyun nan lafiya mu gama lafiya ba tare da ta zane min ke ta sakamu kuka ba kin ji? Kina gani kamar haushinmu take ji din nan?" Itama kasa kasa ta ce" Innata me zai hanna mu kaura gidan amaryar mu yi bikin a cen har a gama? Na tabata hararan da take na sarkar kafana ne da kuma kitson da aka yarfa min, Innata ban san me yasa Innar birni ke haka ba" Kasa kasa ta amsata da fadin" Wuce mu zauna mu nutsu mu gama lafiya , abinda safiya na yi take zuwa bangaren wancen tabi tabin ta sarki sai kuma wani daren, ke dai kafin nan zuwa safiyar ne zamu kama kanmu" Saman tabarmar suka karasa ita kuwa ta gama damawa sannan ta kalli NADIRAH ta ce" Tashi ki shiga ciki kusan gado ki dauko min mazubi, harda na babanki ki wanke su a cen ki bani" Tashi ta yi, sai kuma innarta ta tashi zata bi bayanta Kallonta Fadime ta yi ta ce" Ina zaki je?" HINDU ta ce" Tayata zan yi , na ji aikin da kamar yawa" Da takaici Fadime ta ce" Zauna malama" Hindu ta kalleta da irin kallon nan na ban fahimta ba Fadime ta sake dagowa ta ce" Ki zauna na ce ko Hindu?, Ke kam Allah ya shirya ki, meye na yawa a wanke yan kwarayan da basu wuce hudu ba? Ki dai ringa tunawa yar taki daki zaki mikata , idan ta je tana aikata wani mugun aikin na kazanta ko lalaci babu abinda zai hanna a zage ku, duba ki ga wani shiga a jikinku daga ke har ita, na rasa me Habu yake yana kallonku kunna tsiyar nan, zauna min!" Hindu ta gyada kai ta je ta zauna tana kallon yayarta Kasa kasa ta ce" Aunty, nawama take yar? Ashirin ne fa zata cika, Allah na tuba dama ai da ni zaki mikamu na ringa mata yan share sharen da dan wanke wanken da dan girkin har ta gane , kuma in sha Allahu in bata gane bama sai na ringa safiya ina yi ina dawowa, Allah na tuba abinda da kokarinta, a wuni fa sai ta je rafi sau biyu kuma ta je dandali rai abinta, dama ita bata cika son wahalar sosai ba, to ganu aikin me nake yi?" "Muhammadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallam, ke Hindu ki san annabi ya faku ki gyara halinki, yau ina anfanin mace ba shara, ba guga, ba wanke wanke, bale girki? Ai walahi ba kyau ba ko yar uban wanene sai ta wahala, kika san gidan wa zata je? A cen din zata samu sasauci ko wahala? Ke wani namijin kin san ya fi kishiya masifa, daga ke sai shi a gidan zai zamar maki balaki, bale idan da dangin miji masu jira a yi ? Kunna nan ku a tunaninku kyan da iya shegantakar kadai ke ja ko, kar ki manta talaka kike, yarki talaka take, idan kuka daukarwa kanku wannan hali yaushe garinku zai waye? Kanwata ki ringa tsawatawa Indi, ki ringa nuna mata an ki, ba komai ake nema a samu na, ba kulun take tare da ke ba kin ji?" "Aunty yi kasa kasa kar ta ji ki mana, aunty tsaya ki ji, bari ki ji labari, kun ga yar cen ko? Ni ina ji a jikina in sha Allah sai mun yi alfahari da ita, kuma auntu da kike fadin mu talakawa ne sai me kennan? Mu talakawa ne ama kuma masu rufin asiri a cikin talakawan ma, talaucinmu bai hannamu fara'a ba, bai hannanu bautawa Allah ba, bai hannamu farin ciki ba, bai hannamu hulda da jama'a ba, aunty shegantakar nan kuwa da kike ganni maza da yawa na dauko ta biyu ko ta uku fan ta farkon bata iya shegantaka ba sam...... Allah ma kuwa, ki dai dan bari kawai ki karra Adu'a, ama ko Aminu ne ko? Ni walahi dai dai ya san yadda zai yi da mu duka domin ba zan bari a wulakanta min ya ba!" Ta karashe harda dan buga cinyarta tana kara alamu irin na iya gaskiyarta take fada kennan Salamar Aban NADIRAH ya sakata sake dagowa tana murmushi daga wanke wanken ta ce" Abana ka dawo, dan rike min daya mu kaima inna ta zuba furar nan mu rangada" Yana murmushi harda yi mata sannu ya amshi biyu ya nufo innarta, wace ta saki baki da hanci tana kallonsu Nadirah na bashi labari ya fara kyakyata daria y ajiye kwarayen ya kuma amshi sauran ya ajiye ya juyo ya ce" Shi Aminun?" Nadirah zata yi magana Innarta ta fashe da kuka tana ture furar dake gabanta tana kallonsu gaba dayansu da suka rikice sunna tambayar ba'asin kukan nata Da yatsarta take nuna su ta ce" Yanzu, tsakani da Allah idan muka mace gaba dayanmu fa?, Ko idan wata kadara na tare da ita fa? , Jama'a bakwa gannin sangartar ta yi yawa? Ke Indi dan ubanki je kwaso kayana da na abanki kaf ki wanke su yanzu yanzu ba sai gobe ba, kuma Innarta walahi sai dai ki kauro nan mu zauna tare ama yar cen ko? Yar cen? Sai na bata kyakyawan horon da ba zaki ganeta ba, ! Balen abin nan na kafarki kar na tashi na karya ki, kin shigo birni wata fasara za'a maki dalilinsa?, Abanta abanta yanzu ka riko mata mazubin nan da kanka? Ka riko mata??????" ☹️☹️☹️☹️☹️☹️Tap wollah yau gaba daya in fada maku rubutun ya ringa min gwalo☹️ dan kar na barku shiru ne na samo wannan😍😍😍😍😍 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 1️⃣1️⃣ Sorry ba edditing 😁 Gaba dayansu rasa ina zasu sakka kansu suka yi, ya zamto sai neman gwaruwa suke ciki harda NADIRAH A rikice NADIRAH ta yi ciki ta haska fitilar Abanta ta shiga ciro kayan , duda a hade suke a kule sai da ta fitar da su kaf ta kawo ta ajiye ta je wajen manyan robobin wankin ta dauko ta ajiyesu sannan ta shiga hada ruwan wankin Innarta idannuwanta ne suka cika da kwallah, a hankali ta muke ta shigewarta ciki dan ta dan yau mijin yayar tata ba zai kwana a nan ba, dama idan sun zo yakan yi tafiyarsa wajen mazan gidan ya yi kwonciyarsa, Da ido FADIME ta rakata sannan ta sake maido dubbanta wajen mijinta tana jan hanci ta ce" Yanzu haka kuka zata shiga ta yi dan an saka Yarta wanki ko?" Murmushi ya yi yana sake gyara zamansa yana kallonta ya ce" Wai menene?, Na tabata kukan nan ba haka kawai zaki kwashe shi ba, meye aka maki yau? Me yake damunki?, Duba ki gani yarinyarki ta tsorata ji yadda take wankin jikinta na rawa?, Kin sani sarai wa kuka haifa Dimana, kuma kin san wankin dare ba kyau, me zai hanna ki mata uzuri ta kule kayan cen ta kwonta kusa da mamanta da sasafe in sha Allah ta tashi ta yi wankin?, Kin ji Fadimana?" Ajiyar zuciya ta sauke, domin kukan da ta yi sai ta ji sanyi sanyi a ranta, a hankali ta saci kallon y'ar tata, sai kuma ta dauke kanta kasa kasa ta ce" To ka ce mata ta bari, ni dai ba zan mata magana ba , dan kar ta raina ni" Sai da ya sauke ajiyar zuciya, domin a gaskiya da bata yarda ba bai san ba ko zia iya hakura NADIRAH ta yi wankin nan da daren nan, basuda wuta a bangaren nasu da sai ta yi idan da hasken fitila, kuma fa rikicin Fadime ne, ya tabata akoy abinda ya daga mata hankali , domin har ga Allah yarinyar fa ba laifi tana da kokarin aiki walahi, A sanyaye ya umarci NADIRAH kan ta ajiye ta je wajen mamanta ta kwonta dare ya yi Kai ta gyada ta daure kayan ta ajiye su da ci masu alwashin sai dai a tashi a ga ta gamasu, ita abinma ya rikitata me ya saka mamanta kuka? Sumui sumui ta zo wucewa Innarta ta saka ta dauki furarsu ta kaima innarta su sha Dauka ta yi harda su godiya ta shige ciki Mahaifinta ya yi murmushi ya dake kallon iyalinsa Kamar yadda ya kware wajen yi mata nasiha ya ce" Me yake damunki?" Ido ta zuba masa na dan kankannin lokaci, sai kuma ta girgiza kanta a hankali tana jinginar fa bayanta a jikin garu a sanyaye ta ce" Ba komai Abanta" Sake kafeta ya yi da ido, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya ce" Kin san ta yiwu gobe ace da ke za'a je baban birni ko?" Kai ta gyada a hankali tana kallonsa Ya ce" Kina son zuwa ne?" Kallonsa ta yi da yannayi irin na son gane da gadke yake da tambayar nan?, Sai kuma ta yi murmushi a hankali ta ce" Inada zabi ne Abanta?" Kai ya sada yana dan murza yan yatsunsa, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya ce " Ina iya samun hanyar da zan hanna a je da ke" Murmushi ta yi ta girgiza kai, a sanyaye ta ce" Zan iya, idan har hakan ya tabbata in sha Allah" Idannuwansa ya lumshe sosai yana jin abu mai girma a ransa a kan iyalinsa, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya dauki kasonsa na furar yan murmushi ya ce" Ko dan rakiya ba za'a yi min ba Madame?" Itama murmushin ta yi ta mike ta dauki hijabinta ta ce" Mu je na taka maka mijin Fadime........" Raka shi ta yi sosai sunna hira sannan ya tsaya yana hangenta har ta shige bangarensu kafin ya ja ya rufe masu ya tafi Tana dawowa ta tarar da HINDU zaune saman tabarmar kabar kanta ko dan kwali babu ta nade kafafuwanta tana kallon waje daya Dan murmushi ta yi ta karaso ta zauna a daf da ita tana fadin" Kamar wace kika kulaceni daga fadin gaskiya?" HINDU ta dawo da dubanta kan yayarta, kallonta take yi har sai da ta mata alamu na kallon fa? Sannan ta girgiza kanta tana dankwashi a kanta ya bata kas kas kas ta ce" Gaba daya rayuwar gidan nan so take ta dauke dukkan wani abu mai daraja da kike da shi a rayuwa, kama daga fahimta, fara'a, nutsuwarki baki sani ba" "Ikon Allah daga yiwa yarki fada shine za'a dora min wani abin daban?" Fadime ta fada tana zama daf da ita, domin ta ga ta yi kalar serius, ko menene ba da wasa ta zo mata da shi ba Matsowa ta yi ta kama hannunta ta rike tana kallonta , a sanyaye ta ce" kin san na san ba lamarin Indirah bane ya saka ki kuka, shin me yake damunki da kika kasa fadawa Yaya bayan kunnada kyakyawar alaka tsakaninku, bakya boye masa komai?" Ido ta fara zuba mata, kafin ta waiga wajen dakin da NADIRAH take, ta karra tabatarwa ta yi barci, sannan ta sake dubanta A hankali ta sada kanta, sai ga hawaye ya shiga bin gurbin idannuwanta Muryarta na rawa rawa ta ce" Ina tsoron wata rana na gaza kanwata, abubuwan da nake gani nake ji sun fara neman fin karfin kunnuwana da kuma hankalina da tunanina.........., Bayan neman shiga mutuncina da ake yi wanda na jima da fuskantar haka, shi yasa nake sake lulube jikina da tufafi dan na kare mutuncin kaina da na aurena, a yanzu maganar da nake maki abinda kunnayena suka jiyo dangane da UMUGHLUK ITIFAL nake tsoron kasa rikewa!, Shin me y masu da zafi haka?, Me ya kashe masu ne? UMUGHLUK ai uban kowa ne, yanada kannanun shekaru ama kuma ya dauki girman, ni ba zan taba manta shi ba domin shi ya wanke zargin da ake yiwa Ummu kafin ta rasu, a dazu na ji abinda ke neman tarwatsa min tunanina, na san banida wata hanya da zan iya kare shi sai dai Adu'a, ama ina jin tsoron kar karambani ya sakani tarban aradu da kai, bayan na san banida nasara a kokowar....., Hindu ina ji a cen kasan zuciyata wata rana zan iya shiga uku idan na ci gaba da aikin nan" Hankali tashe Hindu ta ce" Aunty dole ne? Ki bar aikin mana, dan Allah ki samawa kanki sauki , innalilahi wa inna ilaihi rajune wa yake son shiga mutuncinki? Me suke so su yiwa UMUGHLUK ITIFAL? Na zata dan uwansu ne?, " Ajiyar zuciya ta sauke mai zafi ta ce" Idan na bar aiki ba zan iya zama a gidan nan ba, kennan na tafi na bar mijina? Sia yaushe zamu ringa gannin junna? Karshen wata ko shekara?, Idan na bar aikin nan aurena na cikin hatsari!, Kuma da kike fadin dan uwansu, ai na rabaki da giyar mulki, du wanda ya kurbeta ba zai taba sakuwa daga maye ba!" Hindu kam ta rasa me kuma ya dace ta ce, gaba daya auntynta ta sakata a hali na tunani da cikin duhu, ta rasa me ya dace ta yi tunani a kai a yanzu A sanyaye ta ce" Ko me suke takama, zakin sarakai ubansu ne!" Itama a sanyaye ta ce" Haka ne, idan yana gannin fada gaba da gaba ba, idan kuwa ta karkashin kasa ake binsa da sharin fa? Sai dai A'lah ya kare shi kamar yadda yake kare shi a kulun!" "Allah ya tsare shi, aunty, wa yake bibiyarki?" Hindu ta fada Gabanta ya sake faduwa, a hankali ta janye hannunta tana mikewa ta ce" Ki tashi mu kwonta kar mu rasa sallar asubahi a kan lokaci" A dole Hindu ta yi hakuri da abubuwan dake zuciyarta ta je itama ta samu waje gefen y'arta ta kwonta barcin Tunda suka rashi sukai sallar asubahi su biyun suka dinke a daki sunna zantawa tsakaninsu, ita kuwa wannan lokacin ta riika ta matsa kusa da pampo ta darji wankin nan gabaa dayansa A lokacin da mahaifiyarta ta fito dan yin wanka ta shirya ta ganta tana shanyar karshe Da mamaki ta bita da kallo, sai kuma ta nufi pampo dan dibar ruwa a bokici Da sauri NADIRAH ta ajiye ta zo ta tararwa mahaifiyarta ruwan ta mika mata bayin sannan ta koma ta ci gaba da wankinta Wata biyayiyar ajiyar zuciya mamanta ta sauke ta karasa ciki ta yi wankan ta fito Tana kimtsawa tana jin muryar Hindu na fadin ta bar sharar nan ta je ta yi wanka bara ita ta karasa sharar, watau dai sunna ja in ja sunna kus kus ga dukkan alamu gardamar kar ta ji ake yi Murmushi ta yi ta kintsa da kyau sannan ta dauki lafcecen hijabinta ta fito ta ajiye kujerar tayani tsegumi ta zauna tanaa fadin" Kin ga je ki yi wankan ki zo ki je ki amso abin karinmu yi maza".. Murmushi ta yi ta nufi bayin, domin ta mika ruwan tuni , ita kuma HINDU ta gama kamaala sharar ta kwashe taba murmushi ta kalli abin shanyar ta ce" Ka ga yar arziki irin albarka, yarinya mai albarka gaba da baya, ina fata a sallarku ta yauma kin mata Adu'a mai kyau Aunty?" Murmushi Fadime ta yi, kasa kasa sosai ta ce" A kullun inai maku Adu'a ku dukanku, ina fata Allah ya sshiryar min ku, gashi kuwa ashe dai da dan sauki a halayar naku" Murmushi kawai hindu ta yi ta zuba ruwa a roba mai dumi ta zauna ta saka kafarta ta shiga darza, wanda Hakan ya saka Innar birni zuba mata ido tana kallonta da tunanin ita rabonta da ta darji kafarta ba har ta manta ba? Sai dai ta darji ta wasu, watau ta gimbiya ko ta bahija Da dan sauri ta dauki lafayarta mai ruwan dalbejiya ta nada a saman yar doguwar rigarta sannan ta suri kwanon da innar birni ta nuna mata ta nufi fita a ranta tana ayanna' Ban san yaya aka yi hankalinsu ke kwonce a cikin gidan sarauta ba, rayuwa irin ta prison ? Baka isa ka yi kwakwaran motsi idan wani dan Adam din na kusa?, Ai wannan din sam ba rayuwa bace, ukuba ce walahi!, Ina dalili rayuwa ba yanci ba sauki ko kadan?, Ba zan taba irin rayuwar nan ba, ya zamto abinci sai ka zo baban dakin madafa ka amso naku ka juya? Iyayen gidan gidan na hangenku sunna maka maku harara tamkar dabobin da suka siya a kan dole?, Shi yasa ta fi ganewa rayuwar kauye, ta fita ta sakata ta bararake ta wala da ranta ta saki karinta ta hau sama ta fado hankali kwonce, idan ta yi ra'ayi ta yi wanka a teku, ko ta je rafi ta yi, kauyen da ake sako budurwa a gaba dan bata yi aure da wuri ba, kauyen yanzu da sauki, bale Innarta a gefe?ai sai dai ku kashe junna kai da ita!, A hankali ta kai dubanta wajen baban falo, watau falon uwar gidan Sarki Kai ta cire ta karasa tana gaishe da masu kula da madafar sannan ta musamman ka nasu kwanon Mai zubawar ta kama haba tana fadin" Iyeah, wannan dai kamar Nadirar sarkin dogarai?" Nadirah ta yi murmushi tana dan kawar da kanta tuni ta shiga jan wala haula, domin ya zame mata jiki ko dan azalzalar da innarta ke mata a kan haka cewa ko ido hudu suka yi da mutun ta ja masa wala haula dan ba'a san irin mutun ba sam Amsa ta yi tana ji sunna ta maganarta harda mai tambayarta kuma an saka ranar aurenta ko kuwa? Ita fai murmushin dai ta karra basu sannan ta wuce abinta cikin takunta a hankali tana kuma sake kallon bayin dake ta kai kawo ta tabe baki a ranta tana ayana' ku kunna aiki, su kuwa sunna sama?' "Wacece wannan?" Gimbiya ta tambaya daga tsayen da take a jikin babar tagar dakinta tana dan shan Lipton mai dumi dan tuni ta shirya fitowar mijinta wanda baki suka dakatar kawai take jira domin har alkyabarta ta rufa Da sauri wace ke kula da ita da sasafe kafin Innar birni ta karaso ta duba wace ake tambaya Da dan murmushi tana sada kai ta fadi ko wacece, domin a jiya ai sun jima sunna hirar yarinyar, dan kuwa du ta leleka su, yarinya mai dadin hali da kyau kamar ba yar bafade ba Kara zuba mata ido Gimbiya ta yi har ta bacewa ganninta A hankali ta koma cikin dakinta ta zauna saman kujera ta dora kafa daya a kan daya tana kallon waje daya Wani irin murmushi ne ya kubuce mata ta kai dubanta wajen wayarta dake haskawa alamar kira na shigowa Dagawa ta yi ta amsa , sai kuma ta mike da sauri ta idasa hada abubuwan da ya dace ta zuba a jakarta sannan ta ba baiwar nan dama ta dauko suka fito NADIRAH na komawa ta tarar da mahaifanta sunna ta kimtsawa, watau shiri na fita Da mamaki take kallonsu ta ce " Innar birni ga abin karrin fa? Aban birni ina kwana?" Hannunta abanta ya kamo yana murmushi ya ce" Lafia kalau indin innarta, kin ga zamu je Agadaz ni da mamanki, in sha Allah da yama zamu dawo, ki zauna dam kin ji ko? Banda tabin magana" Da dan sauri ta daga kafa tana binsu ta ce" Ama ai baku karya ba fa?" Mahaifiyarta ta dakata daga tafiyar da ta fara domin sun yi bankwana da kanwarta tuni ta juyo ta kamo hannun Nadirah, Gefen fuskarta ta shafa a hankali, ta sakar mata murmushi kadan a sanyaye ta ce" Ai zamu karya, abanki ba zai barni da yinwa ba tunda tare muke, ki kula kin ji yar albarka?" Murmushi ta yi tana gyada kanta tana hangensu har suka fice kwata kwata a balbalin Kwanon abincin ta kalla innarta ta zuba mata Zama ta yi ta turo baki ta ce" Innata, ni bana son cik abincin nan nasu, wainar fulawa nake so da yaji mai dadi, sai kuma , yauwa sai kuma in hau doki" Ido innarta ta zarro tana kallonta ta ce" zo nan yar albarkana mu ci mu gama, sai mu ga yaya za'ayi da maganar dokin, ama wainar fulawa ina muka ganta mu a nan? Bari da rana zan fita na damo maki nono da kaina , na tabata rigimar ba ta wainar fulawa bace ta nono ce" Ai kam, innarta ta gama sanninta ciki da bai, ta saba idan ba karyawa ta yi da sabuwar tatsa ba har wata kasala ke lulubeta, da murmushinta ta karasa suka shiga lamarin gabansu ita da innarta, sunna yi sunna tadi da kyakyata dariya. ( Alhamdulilah, idan har da salatin annabi da wadatar zuci, zaka fi mai kudin farin ciki da kwonciyar hankali, Allah mun gode maka ka karra haskaka mana zukatanmu bijahi Rasulullah salalahu alaihi Wasallam) ______________________________ Tafia ce ta dan kankanin lokaci, duda rashin kyan hanya, da wuri suka karaso GARIN AGADAZ Ba tsaye tsaye suka nufi gidan sarki, sai dai tun daga nesa da hanyar karasawa babar fadar suka fahimci ana wani abin mai mahinmanci, domin taron motoci sun cika wajen sosai Dogarin da ya bada damar a barsu su shige ne yake sanar masu cewa baban taron saukar alku'ani ta ɗaliban babar makarantar islamiyar garin, wace ta yi sunna ta kuma zaga garuruwa dan kwazonsu da kokarinsu a harkar adini Baki ya tabe yana duban gimbiya yana fadin" Ki sauka ku karasa , ni zan je a yi da ni" Itama bakin ta tabe ta kai dubanta daga gaba, inda Fadime ke zaune ta yi gyaran murya *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* . 1️⃣2️⃣ Fadime ta fito tana sake kallon jama'ar zuciyarta na wani irin farin ciki ta bude mata motar sannan ta gyara mata alkyabarta ta amshi jakarta ta rike ta tsaya jiran ta fito Murmushi ta yi ta kalli mijinta, cikin kissa ta ce" FADIME, da ace tana cikin matan da kake iya karrawa, da ka huta Uban gidana....., Matar nan akoy biyaya!" Da sauri ya kalleta, sai kuma ya sake zubawa Fadime ido na dan takaitacen lokaci sannan ya dauke dubansa yana sake hade fuskarsa Murmushi ta yi ta bude ta fita daga cikin motar sannan ta yi gaba Fadime na biye da ita a baya Direct bangaren da ake sauke su ta nufa , domin karya ne walahi ba zata je ta gaisar da matar sarki ba!, Ita din banza ita din wofi, ba zata je ba! Sunna shiga ta karasa tana cire alkyabarta ta yar a nan Da sauri Fadime ta dauke ta karasa wajen makala kaya ta makala alkyabar, sannan ta dawo ta zauna daf da ita ta shiga cire mata safar kafarta sannan ta shiga dan mamatsa mata kafafuwan a hankali a hankali, har aka gabatar da kayan saukar baki Kwanonin take kallo, kwanoni ne da ita bata san ina zata shiga ta samo irinsu ba dan itama a ringa mata anfani da su a bangarenta, yanzu haka tana kallon kishiyoyinta kowace rai bace tana son sannin ina mijinsu zai fita da ita, ama ya masu banza, ta yi murmushi tana girgiza kai, su a tunaninsu fitar gadara ce? Koda yake haka take so su yi ta tunani, watau fitar gadara ce ta soyaya ce Kai ta maida wajen labulen dakin baki, to yaya na masu gidan zai kasance kennan? Ita bata taba shiga bangaren Sarki ba, a kulun tana hasashen yaya nasa bangaren yake kennan? Sake mayar da dubanta ta yi kan FADIME, tana aikinta hankali kwonta, babu rawar jikin nan da son a birge irin na wasu ma'aikatan gidan nasu Sake gyara zamanta ta yi da kyau tana ringesawa kadan a saman kujerar ta alfarma kasa kasa ta ce" Kin kasance mai biyaya a gareni Fadime, kin kuwa san na san da haka kuma ina gani?" Da mamaki Fadime ta dan dago ta kalleta kadan, sai kuma ta sake sada kanta bata ce komai ba Gimbiya ta cire daurin dan kwalinta tana sake lumshe ido dan barci zata yi a hakan tunda ta yiwu su kwana ko kuma idan sun taki Sa'a su ganshi a yau?, A hankali ta ce" Ban san yarinyarki ko tanada BIYAYA wa manyanta ba?" Dan tsam Fadime ta yi gabanta na dukan uku uku, ba dai Gimbiya hasashen saka NADIRAH a layin bayin masarautar garin Tanut take ba? Ai kuwa da ta fadi ba nauyi, domin a wannan karron babu maganar biyaya wa manya, bata cikin wannan, ita ta saba da bautar, zata yi har lokacin da Allah ya cire mata, ama bata tunanin NADIRAH zata iya wannan aikin, sai dai ta yi abinda za'a iya gile kanta walahi! Sunna nan a yannayinsu, sallah ke tashin Fadime, da zarar ta gama kuma zata dawo ta zauna tana jiran tashin Gimbiya daga barci, har aka yi sallar la'asar sannan aka bugo waya cewat ta shirya zasu samu gannin sarki nan da minti talatin Ita dai Fadime na biye da ita har ta gama shiryawar , bata yi sallolin dake kanta ba tace idan ta fito zata yi sannan ta fito cikin shiga ta sabuwar alkyaba tana baza kamshi ana mata jagora har zuwa bangaren baban falo , falon amsar bakin cikin gida Takalmanta ta cire a nan kofa, sannan ta shiga tana jin yadda ake sanar da ko wacece ita, sannan ta kai dubanta wajen mijinta dake zaune barin hagu din Sarki a saman kujera, barin damarsa kuwa UMMA ce zaune ta hakimce tana murmushin da ta tsana a rayuwa tana kallonta Sake gyara alkyabarta ta yi ta idasa shigowa da kyau sannan ta tsaya, ta rage tsayinta sosai ta sada kanta ta shiga miko da gaisuwarta zuwa wajensa Umma ta sake yin murmushi ta kalli ASADEEK, gannin ya gyada kansa a hankali sannan ya sake cire idannuwwansa a kanta ya sakata sasauta zamanta a hankali ta ce" Yin hakan ba laifi bane adalina, yin hakan ba ramuwa bane, idan har ka amshi hakan ka sani an daki tsuntsu biyu ne da jifa daya" Dubansa ya sake kaiwa wajen Bafansa, hakan ya saka bafan nasa fuskantar matarsa ya ce" Ki karaso ki zauna, ki karra bada hakurin abinda ya zamto shirme wanda kika aikata, ki zo ki tabatar masa da bukatarki dan sake wanke kanki!" Wani irin nauyi ya dake dane mata gaban kirjinta, lalle ya zama wajibi ta dauki mataki a kan du wani wanda ke wulakantatata, lalle shawarar da ta yankewa zuciyarta itace daidai da shi!, A hankali kuma wannan mata mai sunna UMMA sai ta kwakule mata idannuwa da hannayenta, bata san wanda ya rigayeka kwonci sai ya rigayeka tashi bane! A kasa ta zauna, ta sake sada kanta, cikin tausasashiyar murya ta ce" Halaya ne irin na mata, shaci fade ne, domin banida tabas, ka yafema bakina da bashida tsaiko wajen yadda muguwar magana Allah ya taimakeka" Kaffafuwansa ya dan murza daya a jikin daya masu dauke da farin safa karkar yana sake sauraronsu baki daya A nutse, cikin fitar harufa a hankali ya dan dubeta ya ce" Ai ba muguwar magana bace, zan iya kiranta da gaskiya" Kai ta karra sadawa tana mai neman afuwa, haka kuma mijinta da Umma na dake tayata neman afuwa Murmushi ya yi, ya ringa kallon Mijinta da ita din kanta, a cen kasan zuciyarsa kuwa tunanin da yake yi shine, shin ko yarinyarsu ta san waye shi tun kafin ya fara sakata fadin abinda bata yi niyar ba? Idan haka ne me kennan?, Tabas shima yana so yarinyar ta kasance wata wace zai iya jin wani abu daga gareta a cikin tunanin dake damunsa a kan bafansa, sai dai yana cikin zulumin idan ya yi haka me ya yi kennan? Ya cutawa yarinyar fa? Me zai iya yi mata? Shi baya anfanar kowa, yana fama da lalura, wai menene a karkashin hadin nan nema? Ya kasa gasgata dan su wanke kansu suka dauke yarsu mace daya kwalin kwal zasu bashi, bayan sun san namiji yake a waje, daga cikin sai a hankali? Mutanen da son kansu yake a bayane ba a boye ba? Kai ya kasa gaskata wannan lamari kwata kwata A nutsensa ya ce" Aunty?" Watau gimbiya, dan haka ta dago tana dan kallonsa Murmushi ya yi ya ce" Yaya zaki iya yin hadin nan bayan babu riba a cikinsa?" Dan daburcewa ta so yi, kafin take daidaita kanta tana kallonsa ta ce" Naw aka zauna da namiji har aka mutu a wannan halin Allah ya karra maka lafiya?" "A wannan zamanin da ido ke tsakiyar kai?" Ya fada shima tamkar ba shi ya yi furucin ba Kai ta sake sadawa ta ce" Ka isa da mu ma, bale ita?" Baki ya dan tabe yana dage kafadunsa ya ce" Hakane kuma" Kallonsa Bafansa ya yi da sauri, kennan ya yarda y isa da su din? ASADEEK ya sake kallon bafansa ya ce" Yaya magana ta hakinta kuma?" Da iya layance abu Bafansa ya fuskanceshi ya ce" Na jima da nema ka bani dama na nemo maka magani, na tabata da tuni yan jikokina na yawo a gidan nan, ama a yanzu ina neman wannan alfarmar, ka bani dama na je na nemo maka magani, ba maganar shiga hakinta tunda muna neman magani, kuma na tabata Allah zai sakamu a hanyar da zamu samu Yarona" Murmushi ya kuma yi mai dauke da ma'anoni da yawa, ya sake dubansa da kyau, ya kalli Umma, sai kuma ya kalli Gimbiya Murmushi ya sake yi sannan ya mike tsaye a kan kaffafuwansa ya sake dubansu daya bayan daya A hankali ya ce" Hakane kuma, Allah bai saukar da cuta ba, sai da ya saukar da maganinta......Bafa ka daura auren kawai..............., Allah ya tabatar da alkhairi" Gaba dayansu ido suka zuba masa na mamaki, Bafansa ya yi gagawar tashi shima yana fadim" Kamar yaya na daura kawai ASADEEK? Aure ai abin a zauna a tatauna ne ko?, Kuma na ga aure mai daraja irin na yar uwarka ai ko sadaki sai mun girgiza mun girgiza sosai ko? Ga saka rana da sauransu?" UMUGHLUK ya dakata ya juyo Lalausan murmushi ya sauke masa ya ce" Ai yarda da na yi cewa, da kai da kaya duka malakar wuya ne ya sakani baka dama, sadaki kuwa ai dama kai kake biya min Bafana," "Ama......?" ...... A hankali ya dakatar da shi ta hanyar fadin" Auta nake son yiwa lesson kafin magariba ta shigo, tana falona zaune, Bafa du abinda ka yanke ka sanar min ta waya in sha Allah, a sauka lafiys" Daga wannan ya shige ciki ya barsu da kallon kallo kowa da abinda ke masa kai komo a ransa Babu wanda ya ce uffan sai bangarensu da suka nufa , shi a gaba Gimbiya a bayansa da Umma Sunna shiga Gimbiya ta fara cire Alkyabarta ta kuma yarwa a nan, a mugun kufule ta ce" Me yake takama da shi a duniya? Mijinta ya kai zaune yana dane nasa bacin ran sosai ya ce" Kudi, da karfin mulki!" UMMA ta zubawa Fadime dake tsugune nesa da su kadan ido, kasa kasa ta ce" Ku iya bakinku, ku fitar da Baiwarku" Gimbiya ta kai dubanta kan Fadime, sannan ta maido kan Umma , a sharar fagen abinda ta yi niya ta ce" Baiwa? Ai baiwama mutun ce, balle wannan tawar amintaciyata kennan, bana darr da magana a gabanta!" Da mamaki Umma ta zarro ido tana kallonta, sai kuma ta juya wajen Fadime wace ita dinma mamakin ya nemi kasheta ta ce" Tashi ki bamu waje zamu yi magana" Mikewa ta yi, sannan ta rage tsayi a nutse ta furta" Ku huta lafiya" Daga nan ta fice Tana ficewa Umma ta juyo wajen Gimbiya ta ce" Lalle gimbiya, baki san a bayi akoy masu baban burin dake iya rikidewa su zamto matsala a tafiyar gaba ba?" Gimbiya ta dubeta da duba irin na ki kuyayeni fa ta ce" Nice kat, domin kema rikidafiyar baiwa ce ta dawo mafi kusanci da UMUGHLUK ITIFAL!, Bama wannan ba, kema da baki zauna a kan kujera kin dauki darasi a makaranta kika iya zagaye bale ni? Idan na yi kwai da zakarana!, Allah ya karra maka lafiya aban Bahija magana nake da ita!" Dubansa ya maida sosai a kanta, Umma kuwa ta karasa ta zauna sokoki a kasan zuciyarta cike da tunanin wannan mata , tan kyautata zaton sai ta yi da gaske a kan lamarinta! Sosai Umma ta lakanci mijinta da sannin wanene shi, shi yasa cikin ruwan sanyi take gasa kishiyoyinta ba tare da ta bari sun san cewa itama yakan zuba mata hauka irin nasa idan ta raya masa, A tausashe ta ce" Lalle ban taba ji hankalina ya tashi, raina ya bace irin na yau ba, ace mu tashi mu zo har masarautar nan, da mu da sauran baki du daya!, Wai yana ba WA'INDA suka yi sauka kyauta shi ga musulmi ko?, Ya bamu damar ganninsa ama a raine a wulakance? Ace kai da kanka Sarkina kana zaune yaron nan na maka magana da gadara da wulalanci da raini?, Lalle abinda ya dace da shi shine wulakanci, ina mai tabatar maka wannan yaro baban wulakancin da ya dace da shi shine mu dauki baiwa mu aura masa a matsayin yarmu!, Walahi sarkina wannan ne kawai zamu yi mu rama wulakancin da ya yi mana, duda baya iya tsinanawa mace komai ama ya zamto mun saka a tarihin rayuwarsa cewa ya taba zama mijin kaskantaciyar baiwa an gama, kafin mu gama da shi kuma sai mun bada dama ya sani sannan ta gama mana da shi?" Wani irin zuba mata ido suka yi su dukansu Da sauri Umma ta ce" Ama Gimbiya kin cika neman fitinar da kanki ba zai iya dauka ba!, Kina nufin zamu yarda a aura auren UMUGHLUK ITIFAL da wata daban da ba yarki ba kuma ya kasa sani??" Gimbiya ta dubeta a kausashe ta ce" kamar da kasa in ji mai ciwon ido, ni inada yarinyar da ta isa ta amsa sunnan matar sarki!, Kuma a yadda na hangi yannayinta tana iya yin kisa a kan yan kudade kalilan, in dai ba so kike a bar maganar kisansa ba sai ki sanar da sarkina na ji!" " Ba haka nake nufi ba, yau babu wanda ya kaini son gannin ya kauce nima na samu cikaken yancin baza abinda bake yi a boye a rayuwata!, Sai dai ina yi ne ina yi mana hannunka mai sanda, domin muna iya kai duka dubu bamu same shi ba a kawowa guda ya tarwatsamu!, Magana muke yi da ASADEEK BRAHAM!, Kuma da kika ce baya iya tsinanawa mace komai kar ki manta, shi abinda yake tare da shi da sunnan wace yake aure a yanzu kadai aka aikata masa da nufin ya fadawa wata ko shima zai samu hukuncin da ubansa yake yankewa yayan mutane dan sun kwonta da wata dan ra'ayi!, Idan har za'a aura masa wata ai dole zamu je mu nemo matar da ta bamu na farko ta sake bamu da sunnan wace za'a hada , dan kar ki aikatawa kanki aikin mugunta da kanki, watau kina gannin kashi da rana, da dare ki zo ki taka!" Umma ta fadawa Gimbiya tana cire kanta a bangarenta, dan ta kula yadda take shayin gimbiya haka itama ke shayinta Kafarsa dake kan cinyarsa yana karkadawa da sauri da sauri ya sauke kasa, wani irin Farin ciki da hasaso nasara da jin dadi a maganar nan cewa a hada UMUGHLUK ITIFAL da baiwa na sheke duniyarsa a farin ciki ya fuskanci matarsa ya ce" Wace baiwa ce wannan kike magana a kanta?" Gimbiya ta saki murmushi tana fuskantarsa ta ce" 🤔🤔🤔🤔🤔🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 1️⃣3️⃣ Gimbiya ta saki murmushi tana kallonsa, hum maza kennan, watau yadda ta lakanci bawan Allahn nan gaskiya zata iya cewa babu wanda ya sanshi irinta, ko haulan fada yake yi ta san me yake isarwa a sakonsa......, Kofa yake a da soyaya suka yi har ta kazance din nan, sun yiwa junna so irin makahon nan Tana murmushin ta sake aro wata kalma dan sake buga zuciyarsa, a matsayinta na mace, tana cike da kishin kalmar, ama a haka ta riketa a matsayin makami dan ta kashe fitinar dake neman kunno mara kai na samun mugun sabani tsakanin mijinta da cilon y'arta mace, itafa mazan basa wani gabanta, ta sani ne sarauta tata ce zuwa gaba domin kuwa mazan manya kaf nata ne, shi yasa take tatala auta dan itama ta samu wajen da ya dace da ita, ta tabata abinda ya ruda zuciyar autarta ba karamin abu bane, ya cencenci jarida! A tausashe ta ce" JINNIN FADIME CE!" Idannuwansa a kan lebenta , tunda ta ambaci sunnan dake girgiza tunaninsa da rayuwarsa baki daya tsayin shekara da shekaru Har wata zufa zufa ta nemi karyo masa a cikin kirjinsa, ya dan kawar da dubansa sannan ya sake kallonta a lokacin da ta yi kalar serius tana fadin" mun jima da rikon Fadime a hannunmu, mun san wacece ita!, A maganar halayanta mun dameta mun shanye mun san mecece ita, a maganar kyau kuwa da kira ko a yanzu da Fadime ta haura shekaru suka fara zuwar mata ai inaga ba boyayan sirri bane cewa kyakyawa ce akoy diri......., Ina mai tabatar maka yarinyarta ta girgije ta fi uwar komai, tsayi ne bai kai cencen ba, ama tsayinta daidai misali ne, ita ta dace da shi ba yarka mai daraja ba!" Naman gaban goshinsa shi kadai ke harhadewa yana kallon matarsa yana sake jimke hannunsa dan daidaita yannayinsa da tunanin abinda ya zamto abin hangensa daga nesa Me? Tana nufin y'ar matar Bafadensa ta fi uwarta haduwa? Lalle idan hakane kamaninta sun isa , sai dai nasabarta! Idan kuwa ya iya boye maganar wanda ya ba UMUGHLUK ITIFAL har ya auri baiwa ya rama kaskantar da shi da yaron ke yi , Wani murmushi ne ya kwace masa, murmushin da ya saka ginbiya sake sakin ajiyar zuciya boyayiya dan samun nutsuwar da ta gaza samu tun jiya, a hankali ta mike ta shige ciki dan shiga bayi kafin su kama hanya, domin wani abu ya rike mata kirji sai ta kakaro shi ko zata ji sanyi sanyi kar ta kumbura a hanya Tana shiga Umma ta dubeshi da duba irin waanda idan bakinta da kumsashiyar magana sai ta yita take jin sauki ta ce" Wani irin yarda ka yiwa uwar wace kake son hada wannan abin da ita?" Sarki ya gyara zamansa yana dage kafadunsa ya ce" Ba maganar yarfa bace, su din bayina ne" "Ka kiyayi lamarin bayi, karamar allura na iya zamewa galma" ta fada tana sake fuskantarsa Murmushi ya yi yana kada kai ya ce" Ki gane, ba zamu tarbi aradu da kai ba tare da mun yi tunanin abinda ya dace ba, basu da zabi a maganar, haka kuma yarinyar bata da zabi a hukuncin da zamu yanke!" Kai ya gyada tana jira, har Gimbiya ta fito suka mimike zasu tafi Rakiya ta masu har bakin mota, a nan ta ga wannan karron Sarki ya ba matarsa umarnin su shiga baya tare da Fadime dan ta yi mata maganar tun a kan hanya, shi fa a yanzu yake da bukatar a yi a gama da wannan yaron ko fili zai zamto nasa! A lokacin da Gimbiya zata shige Umma ta yi saurin rike hannunta tana kallonta ta ce" Ki tabata da zabinki, ki daki maganarki da karfi, domin idan baki nuna a kan haka kowa na iya rasa ransa ba zaki ga shirme, ki kula, domin bana cikin lalatacen wasa!" Hannunta ta fuzge sannan ta daga kafarta ta shige cikin motar Umma ta rufo ta ja baya tana kallonsu har motocinsu biyu suka tafi Juyowa ta yi ta zubawa masarautar ido, nan idannuwanta suka sauka a kan wata baiwa yarinya wace tale bakuwar baiwa ce a masarautar Murmushi ta yi domin yarinyar ba dai sannin hannunta ba Da ido ta mata alamu sannan ta kama hanya ta wuce bangarenta cikin gadara tamkar itace uwa a wajen sarki! Tana shiga baiwar nan na karasowa , dan haka da ido ta kori sauran masu kula da ita sannan ta sabule rigarta tana yi mata wani kallo mai kama da dan iskan kallo kafin ta miko mata hannu suka shige ciki a daidai lokacin da ake kiran sallar magariba (subahanalah, Allah ka rabamu da lalacewa) A hanyarsu ta dawowama basu yi tsaye tsaye ba, mazan nema ke sauka sallah , daf da magariba suka karaso garin su A lokacin da mota ta tsaya Gimbiya ta sake fitar da wani huci na mamakin gannin ta kasa yiwa Fadime maganar nan a hanya bayan haka suka yanke da mijinta A lokacin da Fadime ta fito ta mata rakiya har dakinta tana shirye shiryen yi mata salama ta dakatar da ita tace ta tsaya ta fito Tana shigewa Fadime ta daura Alwallah ta gabatar da sallolin dake kanta domin ji take kamar ta fado daga motar ta yi su a hanyar nan Taba tsaka da adu'arta da yan yatsunta Gimbiya ta fito ta sanar mata tana iya tafia Dukawa ta yi ta yi godiya sannan ta juya ta tafi tana tunanin me ya sa da farko aka tsayar da ita? Watsar da tunanin ta yi domin bashida wani anfani Zama Gimbiya ta yi ta ringa kiran malamanta tana sheda masu kamar yadda mijinta ya kirayeta ya fada mata cewa bai yiwa Sarkin dogarai maganar ba, duda ya san abu ne wanda zai yi murnarsa, sai dai abinda ke boye a lamarin yake so idan lokaci ya yi ya fito masa a mutun kar ya nasa gardama, dan haka du su sanarwa malamansu na tsubu kan su rufe masu baki , watau Dogari da matarsa, duda ta ga kamar hakan wani basu darajar da basu kai bane, a tunaninta sun isa su tankwasa su kai tsaye su amince da komai, ama mijinta sai yake nuna alfarma zasu nuna sunna so, ba zasu nuna cewa za'a yi haka a matsayin bahija ce aka aura masa ba, no, zasu nuna mace ya nema kari shi kuwa ya ga babu wace ta dace irinta, abubuwa dai tsare tsare irin nasu wanda su suka amince da kayansu A yau da darema hira suka sha, bama kamar Hindu da ta tsatsare yayarta da tambayoyi a kan BABAR MASARAUTA, karra karkata kai take tana sakin murmushi yayarta na fada mata irin tsarin masarautar Tana murmushi ta ce" Aunty, kuma kin samu gannin sarki?" Fadime ta zarro ido tana kamma haba ta ce" Gannin sarki kuma?, Da ace na samu zuwa wajen bayar da kyautar masu saukar na tabata da zan hango shi, kin san nima ina so na ga UMUGHLUK ITIFAL ganni na biyu, kawai na duka har kasa na gaishe shi na sake yi masa jinjina irin ta ban girma" Hindu ta karkace kai tana sake dora kankara a saman kitson da NADIRAH ta matse mata kai ta yi mata ta ce" Baki san wani abu ba aunty, ai du ranar da na je babar masarauta, ko ana ha maza ha mata sai na ratsa na ga UMUGHLUK ITIFAL!" Aban NADIRAH dake zaune yana sake nuna mata yadda ake daura damarar hawa doki da kyau dan idan ka yi rashin Sa'a ka hau doki mahaukaci kar ya ilatar da kai ya juyo yana kallon su ya yi murmushi ya ce" An fada maki kamar masarautar nan ce da mule yawo son ranmu?, Ko sarakai sukan nemi damar zuwa ne basa mata shigar kai tsaye, ko a yau na tabata dan a bude take du wanni na annabi na shiga kai tsaye, da ba dan wannan ba na tabata da sai mun jira koda zamu samu shiga, HINDU masarautar dake zagaye da masu kakin sojoji? Dogaransu fa horo ake basu irin na sojoji, dogari dake rike da bindiga? Salarry garesu du karshen wata mai tsoka , dogarensuma sarakin wani kauyen ne nake fada maki, wai inama mijinki?" HINDU ta yi murmushi tana gyara zama ta ce" Yaya ai a nan muka wuni shima ya tatso nonon Indi, yaya dan Allah wata rana ka kaimu mu ga masarautar koda bamu je mun ga sarki ba, ka san me nake son gani? Wannan kofar da aka ce a cikinta gangar dake kuka idan jinnin masarautar ya rabo, wanda aka ce a kulin sai gangar ta yi idan UMUGHLUK ITIFAL ya zo wucewa, ina mamaki, shin tsafi ne ko menene?" Ajiyar zuciya ya sauke zai yi magana ya ga yadda NADIRAH ta cika tana neman fashewa sai kumbura take yi, ya tabata dan sun barta sun shige hirar sarauta ne, murmushi ya yi ya ce" Kin ga Hindu ku zanta da yayarki, ai itama na kula idan abu ya shafi sarautar Babar masarauta ce har sai na nuna na gaji idan ta fara labarinta, bara na iya da yarki" Haka suka sha hira sai da dare ya tsala sosai sannan ya tafiyarsa su kuwa suka kwonta barci Washe gari da sasafe suka fice wajen aikinsu, da nufin sai dare yauma, ita dai NADIRAH da ido ta raka mahaifiyarta tana cike da tausayinta a zuciyarta har ta bacewa ganninta, a irgenta dai gobe zasu tafiyarsu gidan bikin nan na kawar innarta, daga cen kuwa su yi tafiyarsu LABA, ta kagu ta je ta tarda masoyi, barowarta kauyen yana ciwon yatsa da suka je yana ihun kuka innarsa ta koro su tana cewa mai nacin namiji wannan ai sai ta tsotse mata Da! Murmushi ta yi kasa kasa ta ce' Aminu aminuna, iyeah, aminu ina sonka, iyeah........' _____________________________________ Jus din dake ajiye ta sake kallo, gaba daya jinnin jikinta kamar zai tsinke take ji, a hankali ta sake duban Gimbiya dake zaune kafarta na dan girgizawa itama tana kallonta Gimbiya ta sake kallon jus din, ta kalleta ta ce" Baki taba lemun ba fa Fadime?" Gaban Fadime ya sake faduwa, a sanyaye ta sake duban Gimbiya jikinta na karra mutuwa, sosai take son tambayarta ko lafiya? Domin abinda take ganni yana nan girmamar tunaninta, sai dai ta kasa, domin ba yar haka a tsalaninsu ai, sai sada kai da ta yi kawai tana sauke ajiyar zuciya a ranta tana Adu'ar ko menene Allah ya kawo mata shi da sauki A hankali Gimbiya ta dan sake matsota tana dubanta ta ce" To shikenan tunda ba zaki sha lemun ba, dama abinda ya saka nace yau zamu zauna da ke dan ina tafe da gagarumin albishir, albishir din da na tabata shine burinki, shi kike jira, idan kika same shi hankalinki ya gama kwonciya, zaki kerewa Sa'a, zaki samu abinda kike so hankali kwonce" Fadime ta sake dago idannuwanta masu kaifi ta tsare Gimbiya da ido ba ko kyaftawa Gimbiya ta sake gyara zamanta a nutse ta ce" Gagarumin albishir din shine, Mai martaba ya yanke shawarar aurar da yarki wa UMUGHLUK ITIFAL a cikin sirri, wanda kafin a yi haka sai kun kaura daga gidan nan naku kun koma daya daga cikin maka makan vila dinsa, an zuba maku masu aiki, an yantaku yantawa mai girma, an baku makudan kudade ga mota, dukkan abunda kuke tunani na ci gaban rayuwa zaku same shi a kwana kusa, idan har komai ya daidaita nan da sati biyuma an yi an gama!" Gaban Fadime sai da ya rugurguje ya fadi, a zabure ta sake kafeta da ido tana son fahimtar shin wasan kwaikwayo Gimbiya ta koma yi kuma ko menene?, Wannan tsarariyar maganar da ta zubo mata kai tsaye ba kwane kwane ba dan sakayawa da alamu irin na wasan poisson d'avril, ko tace magana irin ta yan maye? Gashi kuma su ba wasa suke yi da junna ba sai kawai ta zamto tamkar mutun mutuni tana kallon Gimbiya, wace ke dan neman damuwa da yannayin Fadime din, dan haka ta sake gyara zamanta ta ce" Fadime?" A hankali Fadime ta sake saka kaifafun idannuwanta a cikin nata tana kallonta, muryarta a cen ciki ta furta" Bahija din, ta ki amincewa da abinda kuka tsarawa rayuwar nata kennan?" Gaban gimbiya itama sai da ya yanke ya fadi, ta sake fuskantar Fadime ido cikin ido ta ce" Ban fahimci maganarki ba, ko kina so ki nunan labe kike min ni da mijina a cikin gidana da y'ayana?" A hankali Fadime ta girgiza kanta tana dan gyara zamanta kadan ta ce" Ba labe bane, maganar ce kuka yi tun karfi, a yanzuma dan ta kama ya saka na fadeta" "Yaya kike min magana a wani tsaye kamar kin samu wata sa'arki ko talaka irinku?" Gimbiya ta fada a kausashe tana duban Fadime, dan ta fara kular da ita, aa, dazu fa na gangare yace mata ta tarbi matar kai tsaye domin a kanta ya kwana, watau ya kwana yana surkulensa da sunnan Fadime din ya tabata ana fada zata hau tsalen hakan, bale an yi magana ta yanta bawa daga bauta? Ai a guje zata amshi wannan tayin har ta duka ta yi godiya, sai dai ga wani raini na nan.shiga tsakaninta da baiwarta bayan ta isa da ita? Fadime ta sauka daga saman kujerar da aka sakata zama ta duka kanta a kasa sosai a sanyaye ta ce" Allah ya huci zuciyarki, ba nufina haka ba, idan na bata maki ki yi hakuri, ama NADIRAH tanada wanda take so, Allah ya karra maki lafiya!" Fadime bata taba zato, ko tunanin zata dauki mari a saman fuskarta a kan wannan magana ba, ku gane ta san ta shiga matsala kennan, ama bata yi tunanin matsalar mai zafi irin wannan bace, mari? Ai mutun mai daraja baya marin fuskar mutun, ko yaro ne ka dali keyarsa, domin fuska daraja gareta, ba'a son marin fusla, bale tata da girmanta da komai wace ta tabata ta girmi gimbiyar? Rai bace kunnayenta suka shiga jiyo mata kalaman da suka sake dagula lisafinta , domin Gimbiya bata tsaya iya nan ba ta nunata da yatsa ta ce" Saurara ki ji, na zauna da ke a nan har na nemi sulhu da ke dan an nunan haka ya dace, ke kin san baki isa na nemi alfarmar nan a wajenki ba domin baiwata kike, tunda kin san maganar bara na sake bude maki ita dala dala, a kan wannan maganar ana iya wayar gari babu ke, babu ubanta, na daukota na daura mata auren na kaita ta cika min burina!, Zata je ne a matsayin yarmu ba taku ba, zata tafi a matsayin Bahijata ba yarku ba!, Idan kika yi hakuri aiki ne zata min na dan lokaci ta dawo gareki, idan kika min gardama walahi baki dayanku a yau ina iya batar da ku na saka ku a halin ha'u'la'in rayuwa ta yadda da kanku zaku nemi a kasheku!, A kan bukatata babu abinda ba zan iya yi ba, na saka auren yarki nan da sati biyu, idan kina so a yi ba ke ki yi gigin bijire min, idan kuwa kina son zaman lafiya ki min biyaya!" Jikin Fadime ne ya kama rawa kar kar kar kar karkamar zara kifa Da sauri ta mike tsaye tana yin baya baya tana kallon Gimbiya har ta samu ta fice ta nufi bangarenta da mahaukacin sauri sauri mai kama da gudu gudu Tun daga nesa ta ringa hango Hindu na tsaye ta daura dan kwali a tsatsonta tana kakaba dariya tana tare tare har dai ta hango Nadirah a saman Dokin mahaifinta mai sanyin hali tana ta wahalar da shi sai aukin fadin CAI CAI take A haukace ta karaso ta damki hannun Hindu tana kallonta ido cikin ido ta ce" Maza ki dauki yarki da kayanku mu gudu!" Daga haka ta saki hannun Hindu ta nufi dakinta da gudu tana wartar dukkan abinfa hannunta ya kai kansa tana cusawa a jakunkunna idannuwanta a rufe Dagowa ta yi zata warci zannuwan Hindu da Nadirah ta ji a riko hannunta da riko mai karfin gaske an juyota A haukace ta saka ihu ta juyo hannunta a dunkule ta kai bugo a kirjin wanda ya yi mata rikon, tana dago kanta ta ga........ 😞😞😞😞 Oh rubutun sarauta ba fai rikici ba *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 1️⃣4️⃣ *NOVEL DINMU MAI TAKEN CARBIN KWAI YANA NAN YANA TAFE CIKIN TSARI DA NISHADI, LITAFIN AKOY DUKKAN ABINDA KAKE NEMA A CIKI, SHAGALIN SAI KA LEKA, KA GARZAYO KAWAI KA SAMU NAKA HANKALI KWONCE😍😍😍, labarin Kwatena ne watau mai BADAKALA DA BAIWATA* A haukace ta saka ihu ta juyo hannunta a dunkule tadakawa wanda ya riketan bugo a kirjinsa tana dago kanta dan gannin ko wanene Wani ihun ta saka mai hade da barkewa da kuka ta jimke hannunsa tana sake kallonsa ta bude baki jikinta na rawa ta ce" Mu tafi, mu tafi, idan muka tsaya zasu fito mana da rikicin da ya fi karfinmu, kana ji barazanar da ta yi min cewa zata iya batar da mu, ko ta saka mu a ukun da mu da kanmu zamu nemi a kashemu?, Ita tana son y'arta har haka ni zata saka min ya a uku? Da UMUGHLUK ITIFAL take magana, yata zata mika dakinsa a matsayin y'arta? Duk ranar da hakan ta bayana da kansa zai zo ya tsire mu a jikin kanta, mu da kanmu sai ya mayar da maganarmu rikicinsa, bana ciki, babu maganar alkhairi, da ace magana ce ta alkhairi abin farin cikina ne, abanta, mu gudu ka ji?" Sake riketa ya yi a hannayensa a hankali ya janyota jikinsa ya rukunkumeta shima jikinsa na wani irin rawa tamkar zai kifa Gab gab gab haka jikinsa yake yi, muryarsa a matukar raunane ya ce" Marinki ta yi ko?" Tana cikin gunjin kukanta ta gyada kanta, numfashinta tamkar zai dauke dan tsoratar da ta yi, tunda take , tunda ta taso ba'a taba daga hannu aka sauke mata biyar ba sai yau, ikon Allah A hankali ya ce" Muna zaune mijinta na min maganar da ta maki ta fado tana sanar masa cewa ba zamu sauraresu ta laluma ba sai ta tsiya domin ita yanzu har marinki sai da ta yi da ranta ya baci, ban san dalili ba, ni dai na ga irin bacin ran da ya nuna har ya bani mamaki, domin a nan ya dauke fuskarta da mari har jikinsa na rawa......, Zahrau ban san dalilinsa ba, ama irin yadda ya nuna bacin ransa ko ni sai haka, a cikin fadansa ne ya manta wayon da ya so yi min ya fada min cewa idan muka yarda aka yi auren nan na dan lokaci ne zaki kawar da UMUGHLUK ITIFAL ki dawowarki wajenmu......., Wannan abu shi ya rikitani ya sakani kuka......." A hankali ya karashe yana kifa kansa a kafadarta ya ja wani irin numfashi hawayensa suka sauka a saman hijabinta, sannan ya karra matseta a jikinsa sosai ya ce" UMUGHLUK ITIFAL, sarki ne mai koyi da manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam , shi din bawa ne mai jin kan wanda yake wajen masarautarsama bale na ciki tsundum, UMUGHLUK ITIFAL idan ke bai kara ki ba ni ya karra ni, idan bai karra mu ba to fa in muka fita waje muka yi shela ya karra dubanmu, Fadimata na rantse da wanda raina ke hannunsa idan akace a yi fito na fito a yakin da ba za'a dawo ba dan a taya UMUGHLUK zan je ba tare da na yi tambayar menene ba'asin yakin ba, domin na sani ne shi din mai yi ne domin Allah ba dan ya karre kansa ba!, Zahrah ko ke bakya jin haka a ranki ne?" Itama tana kukan ta ce" Haba Abanta, idan akoy masu takama da sunnansa idan sunna maganarsa ai bayana suke!, Ko a yanzu da ace wata magana ce ta zuciya daya, ciki harda NADIRAH ta kasance baiwa a masaraitarsa, bani da darrrr zan saketa ta je da Adu'ar tsari, domin na san koda an sakata cikin halin kaka naka yi kafin ya yi zagayen karshen mako ne zai kwatar mata hakinta!" "Nima abinda na sani kennan, sai kuma furucinsu ya gigitani!, Ki sani maganar batar da mu bata gigitani ba, domin ni bawa ne, mai sallah, wanda ya yarda da kadara, na tabata idan duka duniya zata taru dan ta cutar da mu sai idan Allah ya aminta, idan Allah bai yarda ba, babu wanda ya isa ya yi mana koda kwarzane ne!, In kuwa kadararmu mu gama da duniya a haka ne muna dakinmu A'lah zai kawo dalilin fitarmu!, Wannan magana kamar tsarin film? Basu tashi hawanmu ba sai da suka nuna mana dukiya, lalle basu sanmu ba, a shekarun da muka yi a karkashinsu da wannan ne a gabanmu da mun taka wani mataki mai girm, domin da mun kasance bafadai masu hada husuma dan su samu na kashewa!, Sai Dai Zahrau Uban marayu ne zasu taba!, Zahrau hakan na nufin idan bamu amince din ba, zasu samo wani wanda zai amince din, hakan na nufin idan har muka kiya din, zamu zo mu tardo abu goma da gomi ya tara na halin ha'ula'i a gabanmu!, Zahra hakan na nufin munna da hannu a dukkan abinda zai faru" Idannuwanta ta dago da tuni suka yi hulu hulu tana kallonsa ta ce" Idan muka amince din, hakan na nufin mun kasance cikin masu mugun nufi dan mu cutar da shi? Idan ta je nesa da mu, hakan na nufin mun saketa a dokar dajin da ta yiwu wata rana su yi galaba a kanta har ta aikata abinda suke so? Abanta kar ka manta yarinya ce ita karama, wace ake iya yiwa barazana da rayuwarmu ta amince da ko menene kai tsaye dan kar a cin mana!, Sannan ita din tunda ta zo duniya ta ki jinnin gidan sarauta da abinda ya shafe shi, ko a jiya ina ce sai da ta yi maka hirar Aminu?" A sanyaye ya sake riketa a jikinsa yana rintse idannuwansa ya ce" kin fi kowa sannin na fi ki shakuwa da kulafurcin NADIRAHNA, kece ke min nasiha a kan soyayar da nake nuna mata, a yanzu haka wannan shine abinda ya dakatar da ni Innarta, a yanzu haka wannan din shine abinda ya zamto min katanga da daukan matakin amsawa kai tsaye, yaya zata dauki maganar? Yaya zata iya amsar maganar? Domin idan har hakan ce zata kasance sai na fuskanceta na sanar mata gaskiya, koda kuwa hakan zai zamto ajalina!, Innarta, shekararta kwata kwata ashirin babu yan watanni a duniya, yaya yarinyata zata iya daukan wani nauyin? Na tabata akoy abinda ya tunzura su daukan wannan matakin!" A sanyaye ta sake dubansa, ta rage muryarta sosai domin tana hangen Hindu dake kai kawo ta dan leko su ta koma kamar zata saki zani dan rikita A hankali sosai ta ce" Bari ka ji abinda yake faruwa......................" Gaba daya ta dauke duka kaf abinda ta sani wanda ya saka gimbiya da mijinta daukan matakin bada yarsu daj su wanke kansu, abin ya zo da rikicin nan n yar ta kiya shine gimbiya ta zame y'arta take neman tura NADIRAH Sosai hankalinsa ya sake tashi, ya rasa me zai ce , da kyar ya iya zama yanzun ya zamto itane a tsaye jikinta na rawa A hankali ya nuna mata daf da shi sosai, ta zauna tana sake dora kanta a gefen damtsansa A sanyaye ya ce" Ina cike da tsoro Fatina, kin ga ina jin tsoron halin da yata zata iya kasancewa a ciki, ina tsoron fuskar da UMUGHLUK ITIFAL zai duba idan ya gane cewa NADIRAH ba itace aka bashi a matsayin mata ba, duda na tabata ya aminta da wannan hafi ne dan shima da wani abin a kasa, domin na sani sarai dan kar a zage shi ko sirrinsa ya fito fili ba zai taba yarda ya kashe rayuwar wata ba!, Haka kuma ban san yaya yata zata rayu a cen ba, shin zata iya kaucewa cutar bawan Allah ko zata kasa?, Abinda na sani shine yarinyar cen ita daya na malaka, kuma ina son abita fiye da kaina, a kanta ina iya yin komai, sannan a yanzu da na ji maganar dake boye a cikin son su mayar da ita matar SARKI, sai na ji dama ace zan iya na yarda ta je, da zuciya daya ba dan sarautarsa ko arzikinsa ba, ta kasance wata jigo a rayuwarsa? Ko ita din wata mahadin rayuwarsa ce?" Hindu dake kofa a tsaye kamar ta afko ta sake daga labule ta musu kuriiiiiiiiiii, a dole summa suka kallota Gaban goshinta ta murza sosai ta ce" Yaya mu fece din ne ko kuwa?" Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya ce "Hindu zo mana" Ai kuwa kamar jira take ta shigo da sauri, sai dai gannin sunna kallon kofar ya sakata juyawa da sauri Haba ta kama ta juya tana fadin ina zuwa Karasawa ta yi ta kama hannun NADIRAH ta mayar da ita wajen zaman ta sake bata doguwar wukar babanta ta ce" Ki zauna a nan mana yar Hindu ba kyau labe ina zuwa, wannan riketa du wanda ya maki eh yane ki auna masa yar albarka ina zuwa" Kai ta gyada hankalinta gaba daya a tashe , har yar yatsarta ta gurde wajen dirowa daga kan dokin babanta gannin mamanta na rusa kuka, kuma sai ga babanta ya wuce fuuuuuuu shima, shine Hindu tace ta zauna ta jiyo masu, kuma gashi ita ta ji ama ta hannata labewa ta jin itama Komawa hindu ta yi tana sake zuba masu ido Gannin da gaske kukan mijin yayarta ya yi shima sai ta nemi rikice masu, ta yi zaman yan bori tana dabar kai ta fashe da kuka ta ce" Wayo mun shiga uku,wani abu ba ka yi za'a yanke maka kai? Ko aunty ke kika yi wani abin? Ku tashi mu gudu idan laifi kuka yi ba zan rasa wajen boyeku ba babu wanda zai same ku,wayo ni Hindu kunne uwata, kunne ubana me ya aikeku aikatawa sarki bafan UMUGHLUK ITIFAL laifi? Kun sakani a uku ni da yar marainiyata? Innalilahi wa inna ilaihi rajune mun shiga uku!" A hankali Fadime ta kalli mijinta a sanyaye ta ce " ka tabata wannan hirar ta ayi ce da Hindu?" Shima idon ya kura mata yana kallo, bama irin yadda take turbuna kaffafuwanta a cikin kasa ba ta yarda dan jonanen dan kwalin kan nata a kasa kamar kace fit ta fice a dubu kota yi ciki da kai Ajiyar zuciya ya sauke ya sake rike hannun matarsa a hankali ya ce" Hindu ki nutsu mana, babu fa abinda muka yi" Hindu ta dakatar da kukan tana sake kallonsa ta ce" Kuma kake kuka? Yaya me zai zo maka da karfi ya shirgaka a kas fisabililahi? Aunty hala kukan amare ya yi? Wayo ni wayo kaina ni Hindatun Habu makadi!" FADIME ta gyara zamanta tana jan hancinta ta ce" Ka daina batawa kanka lokaci, babu abinda bata ji ba, ka je kanka tsaye kawai Abanta" Da mamaki ya zubawa Hindu ido ya ga sai micui micui take da ido da baki ta kalle shi, ta kalli FADIME Kai ya gyada yana sauke ajiyar zuciya ya ce" Yaya kike gani , me ya dace mu tsayar? Mun rasa ina muka dosa" Sai da ta yi murmushi ta gyara zamanta kamar ba ita ke share sharen hawaye ba ta dube shi ta ce" Matsalar da ta dan sage min gwuiwa har na koka din nan daya ce kwalin kwal, yaya shi zakin sarakan da bashida anfani?" Sai da suka zabura sunna kallonta su dukansu Harshen zaninta ta saka ta sake share hawaye ta ce" Na tabata sihiri ne bawan Allah na san ba uwa ba uba ba dangi masu jin kai, ama ba komai idan muka je in sha Allahu zan ringa dan bada taimako na karya tambaya da tashin tsakiyar dare ina kama sunnansa ina li'ilafikuraishi, in sha Allahu zai dawo mai anfani, in kuwa abu ya gagara sawayenmu a likafa zan nado yata mu yi LABA, tunda ai du dadin riga bata yi ya wuyan hannu ba" Da takaici Fadime ta ce" Dan Allah ki saurara da magana rututun nan haka, ke kinma gane me ake nufi ne?, Haba dan Allah Hindu me zai saka a yanzu da hankalina ke tashe ki karra tayar min har na fara tunanin ko kin haukace ne?" Hindu ta dubeta ta ce" Ni kuwa nake da hankali, ras nake tunda ni a bayane nake gannin wasan!, Bari ki ji, idan kuka kiya da maganar nan ku tabatar cewa lalle zasu batar da mu din, domin kuwa har Habu da ya auri Hindu kanwar Fadime sai an halaka da makotan Hindu bale wata hindu kayan banza da yar yata da bata taka kara ta karya ba, a cen kauyenma neman inda zan gudu da ita nake yi dan Innar Aminu ta tsaneta Aminu kuwa ya yi mata asiri shege wuya uwa marikin lema!, Na takaice maki ta kife ko ta walare ni inada amsa wa UMUGHLUK ITIFAL, zan rusa na makoki ne na fada masa cewa wuka aka dora a wuyanmu cewa ko mu aminta da auren nan ko a karmu kuma ba za'a daina neman wace zata je ta karshi ba, muka ga mu masoyansa ne gwara mu shigo daga ciki, shi Habu sai a san yadda aka yi a mayar da shi makadain babar masarauta sai a bamu bukarmu mu rabe, a haka sai a raraka kafin Allah ya bamu Sa'a a kansu, domin kin ganni nan sai inda karfina ya karre walahi, numa fa yar gani a kasheni ce a kan Zakin sarakai, aure mun yarda ba sai an kashemu ba!" Ikon Allah wanda ba'a saka masa rana, kallonta kawai suke yi, yadda take magana da karfinta gaba dayansu gani suke yi bara san irin abinda tske neman saka kanta da ita da yar tata ba Jiki a sanyaye ya ce" Da ke za'a tafi gidan na yarki?" Fadime ta yi dan tsaki tana dafe gaban goshinta dan takaicin HINDU ba zai taba kasheta ba walahi! HINDU ta yi wani murmushi watsar tana kallonsa ta ce" To kai zaka rakata yaya? Ka san dai ba za'a je da kai ba, ka bari idan muka sayi gida sai ka kauro ko?" "Innalilahi wa inna ilaihi rajune, abanta dan Allah ka tashi ka nemi wanda zaku yi shawara, idan kuwa bari zaka yi sai dare ya yi ka fitar da mu mu samu mu gudu to, ka daina magana da Hindu, hindu fa tunaninta daban da na mutanen kirki!" Fafime ta fada tana neman fashewa da kuka, ita kuwa Hindu ta tabe baki tana gyara zamanta , ita gani take auntun tata ce sam bata gannin me take nufi, ai walahi ko ana ruwan muzuru ba zata yarda a tafi da yar nan ita kadai cikin mayu ba!, Ina, ai tass za'a je da ita, basu sanni bane , basu santa bane walahi, ba zata taba yarda a dauki Nadirah a mikata ita daya ba, koda sun yi haka ita zata je daga baya a matsayin yar shishigin bayi! A hankali Aban NADIRAH ya dakatar da matarsa dan baya so su fara fada a yanzu da zuciyarsa ke karye, bar ga Allah yana iya yi masu kuka A sanyaye ya ce" To Hindu yaya zaki yi da yar taki? Ta yaya zaki shawo kanta?, Yaya zaki yi da hakkin Aminu? Shin kunna cin kudin Aminu kuwa?" Caraf Fadime ta cafe ta ce" Ahaf, cin kudinsa ai sai dai kar a kuma kaima malan walahi da wani zance kake" "Ki yi shiru mana Fadima menene haka ne?" Aban Nadirah ya fada a sanyaye Hindu kuwa ta yi tsuru tsuru tamkar zata kifa A hankali ta ce" Na shiga uku, riginar duka a Indina da Aminu take innalilahi " Ta kalli Fadime ta kalli Aban NADIRAH A hankali ta ce" Walahi ni dai ba zaku aikani fada mata ba in dan wannan nema kuke min rarashi ba zan je ba, yi abinda tace sai ta gudu idan aka hanna mata Aminu? Ai aunty ce kadai zata iya wannan aikin dan walahi abanta kaima kuka zaka mata dan na kula baka hanna kanka kuka yanzun, babu mai hadani da yata walahi" ta karashe tana sharar hawaye na gasken gasken ta dora da fadin" kuma mu bama cin kudin Aminu, Allah na tuba gori ba kyau ni fa na dora masa teburin da Indirah tace a bashi jari, kuma babarsa yanzu haka wannan cirar da kuka ga na mata mun gudo a bakin da baya karya na hi ance babarsa ta kai jaka uku da rabi kudin an gani ana so na yar makotansu, ai ba wani ciwon hannu da yake ihun ba zata masa auren dole bane ya sa na gudo da yata dan na shiryawa kowani dan iska da kyau, ni dai yanzu ta yata nake ba ta rigima ba da kike nemana da fada!" A hankali Aban NADIRAH ya ce" Ku daina rigimar nan mana dan Allah, innar Indi kina nufin shi Aminun na Indinki ne za'a yiwa aure? Ya Allah " Hindu zata yi magana muryar jakafiyar cikin gida da muryoyin maza biyu ta karade gidan da salama A tsorace Fadime ta fara mikewa, hakama mijinta, bale da suka jiyo muryar NADIRAH tana fadin" 🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* *LABARIN UMUGHLUK ITIFAL, BAN DAUKO SHI DAN CIN ZARAFI WA KASATA KO JAMA'AR KASATA BA, SALO NE NA MARUBUCI DAKE BUDE TUDU DA GANGARE DAN HADEWA A MAHADA GUDA, KO KUSA BAN GOGI ADALCI DA KARAMCI IRIN NA SARAKAN KASATA BA, NA KAMANTA RUBUTUNA NE A SAMAN IDEA DINA DAN KAWAI NA ISAR DA SAKONA DA KUMA SALON ALKALAMINA, IDAN HAR A RUBUTUNA NA TABO MASARAUTAR GARINKU KUMA ABINDA YA HAU KANTA BAI MAKU BA , KO YA YI DAIDAI DA HALAYAN DA KUKE FUSKANTA KU SANI BAN JE NA BINCIKA BA, BAN KUMA YI DAN NA CI ZARAFI BA, NA DAUKI ALKALAMINA NE NA KUMA YI AIKI DA DAMATA NA KASANCEWA YAR KASA, VIVE L'INDÉPENDANCE, VIVE LE NIGER, MERCI* 1️⃣5️⃣ A tsorace Fadime ta fara mikewa, hakama mijinta, bale da suka jiyo muryar NADIRAH na fadin" Aa gwara dai ku dakata din innata tace wanda ya wuce na wuce da shi, sirri suke yi" Da rarafe HINDU ta fito tana lekowa ta ce" Ke zo nan zo" a ranta kuwa tana ayana 'na shiga uku Gimbiya da sara suka, kar ta ja a fasa' Muryar Jakadiyar ne tana fadin" Ke kauce mana daga hanya ko mu babalaki aikomu aka yi wajen sarkin Dogarai!" Ya saka Abanta saurin fitowa yana dubansu yana kakaro murmushin dole ya ce" Jakadi yarki ce, ta wajena NADIRAH " Da mamaki ta sake kallon NADIRAH dake tsaye tana sake turo baki Murmushi ta yi ta furta" Masha Allah, Allah ya raya ya fitar da miji mai takaici" Hindu kawai ta amsa sannan ta kama hannun NADIRAH suka shige daki suka zauna sunna kallon kallo Jakadiya ta sake gaisar da su da mutunci, domin su din mutane ne da suka san darajar kansu kuma suke kiyaye dukkan abinda zai iya zubar masu da mutunci, Bayan sun gama gaisawa ta dube shi ta ce" Mai martaba ne ya turo mu da kansa, yace ace da kai yana wajen sirrin da ka sani, ka je masa da sakon GAGARA yana son gannin idan ya cencenta, yace a ce da kai yana kan bakansa, maganar na nan daram yadda aka yanketa, yace ace da kai yana jira" Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya amsata, yana kallo har suka tafi sannan ya koma yana kallon Fadime dake tsaye ta rungume hannayenta a gaban kirjinta A sanyaye ta ce" Ana nufin, a tafi da ita bangarensa ya ganta?" Kai ya gyada ya zauna a nan yana kallonta Murmushi ya yi ya girgiza kansa ya ce" Anya na yi maku adalci kuwa? Anya ni din uba ne na gari kuwa?, Anya da na zauna a nan ina aikin nan na maku adalci kuwa? Sai nake jin dama dako na je na yi na ciyar da ku, sai nake jin dama buka na samu ko a ina ne na saka ku, na kasance tare da ku, anya ni din nan uba na gari ne kuwa?" A hankali Fadime ta karaso ta tsuguna tana kallonsa, ta ce" Kai uba na gari ne Abanta, kuma kai miji na gari ne....., Ai inaga da saukima, ko menene inaga an dan rangwonta mana fa, domin da wani karnin ne mu din za'a fara batarwa, kashewa ko badawa a duniyar mahaukata, sannan a dauki y'ar a sakata a mugun aikin!, Abanta ina cike da tsoro, ni bana tsoron sanar mata domin ni nan zan sanar mata, abinda nake tsoro shine kar su rinjayeta, yarinya ce!, Ama in sha Allah, Allah zai kama mana, ni na yi imanin adu'armu ba zata taba faduwa kasa ba, in sha Allah zamu yi ta rakata da Adu'a, ko menene zai zo da sauki, bi'izinillah ba zata aikata abinda suke so ba, .....ka kwontar da hankalinka, a yanzu ka samu ka je da itan, idan kun dawo zan fita da ita, domin bana son abinda zai janyo mana saka ido, zan fuskanceta na fada mata gaskiya, mu da muka rike Allah? In sha Allah shi zai kama mana, shi zai daidaita mana, shi zai kare mana yarmu, kar ka sake sage min gwuiwa bayan na dangana Abanta" Ajiyar zuciya ya sauke ya gyada kansa ya ce" A saka mata hijabi da nikaf mu tafi" Ciki Innar birni ta koma ta zakulo lafcecen hijab dinta da nikaf dinta ta ba Nadirah fuska a hafe ta ce" Ke saka maza ki tarda babanki ku je nan ku dawo" Sakawar ta yi ta fice suka tafi Sunna tafia innar birni ta zauna ta fuskanci Hindu, a ttausashe ta ce" HINDU, ina so mu yi magana dan Allah, ta fahimta, ina so ki bani duka kaf hankalinki kin ji?" HINDU ta zauna daga ninke kayan da auntyn tata ta barbazo tana kallonta Fadime ta ce" HINDU, ina so ne ki fuskanci abin nan da fuskar da ya dace, ina so ki gane cewa a tafiyar nan rikicinta ya fi jin dadinta yawa, kuma ki sani ba za'a taba yinta da ke ba domin uwa ce ke, jinnina ce ke, Gimbiya ba zata taba yarda ki je ba, dan tana iya gannin zaki hannata aiwatar da abinda suka yi niya ne" HINDU ta kalleta , alamu na hankalinta ya fara tashi da maganar karara ya bayana a tatare da ita Muryarta a sanyaye ta ce" Ita daya? Ita daya za'a kai babar masarautar da sha yanzu biya yanzu idan aka kamaka da wani laifin? Ita kadai za'a mika wajen da take da kishiya? Yayya kishiyar take? Ita kadai za'a kai wajen da wasu zasunna zuwa sunna azalzalata aikata sabo? Idan fa suka cin mata?, Yaya zamu yi?" Fadime ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Shi ya da da farko na so mu gudu, ama abinda kika fada din nan ki sani ya yi tasiri a zuciyata, na tabata dalilin wannan har makotanki sai sun shiga uku ba ke ladai ba, da a yi wannan gwara mu zuba ido mu rungumi Adu'a mu barawa Allah zabi,Hindu tabas abin nan ko uwar mata sai wace ta ginnu a kan kafafuwanta zata iya, sai dai kuma yarinyarki tanada adu'o'in neman kariya daga dukkan fitina, haka kuma tarbiyara da muka bbata ba ta kwadayi ko ta alfahari bace, sai mu dangana mu sake dukufa mu ringa fadawa Allah, na tabata wata rana idan da rai zata yi nasara, idan kuwa kadarar NADIRAH ce haka ina fatan kafin su cin mata ta yi kisa ita nata ran ya bar gangar jikinta........." Fadime ta karashe tana lumshe idannuwanta hawaye naa digowa daga ramin idannuwan nata Itama HINDU, a hankali kuka ya zo mata, kuka mai rauni, mai matukar zafi, domin a da kwata kwata bata hango lamarin nan a haka ba, a yanzu da akai mata irin wannan karatun sai ta ji hankalinta gaba daya ya tashi tana neman ficewa daga hayacinta, tabas ba zasu taba yarda ta bi y'arta ba, a yanzun sai take ji dama basu zo birni ba, da zuwa ta yi ta ba innar Aminu hakuri aka yi auren nan, innalilahi wa inna ilaihi rajune, tabas abin na nemen rikitata, sai dai yayarta ta yi ta tausarta da nuna mata cewa basu da makamin da ya zarce Adu'a, ana karni na yanci kai ne, ama kuma karni na mai kudi shine sarki, bale sarkin da kansa a kan bafadensa? An yi wanda ya fi wannan zafima. An dauki kusan awa daya da tafiyarsu sai gasu sun dawo, dawowar da suka yi a cikin mota mai sirri, watau mai bakin gilashi, da direba daya kwal su biyu a baya Bai masu dogon bayani ba, ya taya su kwasar dukkan abinda yake na anfanin gagawa a garesu sannan suka bi shi bisa umarninsa suka shiga motar nan direba ya ja su, Tafia ta dan lokaci kankanin da bai fi minti talatin ba suka karaso wani gida mai babar kofa da tsari irin na masu hannu da shuni , suka shige bayan ya sauka ya bude masu sannan suka yadda zango a sabon gidan babu mai yiwa dan uwansa magana sunna jiran abinda zai biyo baya, domin ko NADIRAH da ta tambayi innarta cewa nan kuma ina ne? Yaushe zasu tafi wajen bikin? Amsar da ta bata shine ta yi shiru bata son hayaniya yau, hakan ya bata mamaki ya kuma daure mata kai, innarta bata son hayaniya? Lalle akoy abinda yake faruwa, sai dai zata zuba masu ido ta ga koma menene A gidan sarki kuwa da gadara ya yi kiran Gimbiya, a lokacin matarsa amarya ce ke tare da shi tana zuba masa abinci, a dole ta fita dan zai yi sirri da Gimbiya, zuciyarta cike da daci Gimbiya na zuwa ta zauna saman kujera fuskarta a cinkushe, yau tunda safen nan da ta dauki mari take bangarenta kamar zata kone dan bacin rai, Dolema ta rikita rayuwar FADIME, ta tabata ta amshi mari daga mijinta ne dan ta mari FADIME ba dan wani laifin daban ba, mari a matsayinta? A gaban bafadensa?, Lalle lalle idan komai ya lafa sai ta yi dalilin da Fadime ta dawo yi mata bauta dan ta wanka mata ninkin ba ninkin din marin da mijinta ya yi mata! Jus din da ya kai bakinsa ya ajiye bayan ya shanye ya gyara zamansa yana fuskantarta ya ce" Elle est tres belle, mais sauvage, l'a tu remarqué ?" ( Tanada mugun kyau, sai dai batada wayewa, kin kula da haka?) "Wayewa, abu ne mai saukin koyo, duda jahila ce zai dan bada wahala sosai gashi waje a kure, rayuwar sarauta ce mai wahalar dauka Aban Bahija!" Gimbiya ta fada a tausashe tana sako sunnan Bahija dan ta ga reaction dinsa, domin rabonta da ta sako magana irin haka an jima Juyowa ya yi daga kunna TVn da ya yi ya dubeta ya ce " Ba jahila bace, saukarta biyu in ji ita" Baki ta tabe tana dubansa ta ce" Islamiyar kadai ta je, bata da boko" Kafadunsa ya dage ya ce" Sai a gargadeta da budar baki da yin magana ko a gabansa ne, dan kar hakan ya haifar da matsala, an kai su gidan BAHIJA na yi magana da Lauyana cewa ya mayar sunnan mahaifiyarta a saman takardar" Da mamaki ta zuba masa ido, a hankali ta ce" Gidan BAHIJA?" Kallonta ya yi a kausashe ya cire idannuwansa da kansa ya mata alamun kwarai haka yake nufi Zuciyarta sai da ta yi wani irin tsale ta daki kirjinta dan buguwa da faduwar gaba, sai dia bata yi magana da karfi ba dan ta kula ya fita hawa sama yanzu A tausashenta ta ce" Ama gidan Bahija fa ka ce Aban Bahija?, Gidan da ka kashe makudan kudi million na gugar million la ginna shi?, Gidan da ka yi masa hawa hawa hawa ka zuba gazon ka yi masa ginnin a zo a gani kace na Bahija ne saboda ita daya ce mace cikin yayanka itace abin tausayi, sauran su nemi nasu maza suke shine zaka saka sunnan wata a sama?" A kausashe ya ce" A da ba, a da da nake tunanin na isa da ita, a yanzu gaskiya kowa ya yi ta kansa kawai tunda har ni zata duba ta yiwa rashin kunya!" "Aban Bahija, ka kiyaye, kar son zuciyarka ya fi karfinka wannan karron, domin ka san abu ne da ba zai taba yiwuwa ba, kar girma ya fadi a kan abinda bai kai darajar haka ba!" Ta fad a dan kausashen itama, domin abin ya fara bata tsoro, gidan Bahijarta? Gidan da take takama da shi a cikin kishiyoyi? Bama a lokacin da ake kan ginninsa basu isa su hadu da ko daya ba sai ta yankawa mutun magana, bale a yanzu da aka gama? Da gadara gadara take dauko maganar gidajen sarki tace kaf ciki gida uku ne ya fi na Bahijarta? Lalle akoy tashin duniya a garin nan! Zamansa ya gyara da shauki irin na yan duniya ya ce" Kina tunanin da abinda kike tunani ne gidan nan zan malaka mata?" Kai ta juyar ta sake kallonsa ta ce" To nima shi na gani, me zai hanna ka saka sunnan Uban yarinyar idan ya so idan aka daura aka tafi da yarinyar sai ka maido sunnan Bahija a sama?" Habarsa ya kama da mamaki ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 1️⃣6️⃣ Jinjina da ban girma zuwa a gareku masoya, Allah ya karra lafiya da nisan kwana da rufin asiri amen Habarsa ya kama da mamaki ya ce" Ke maman Bahija ki ji tsoron Allah, in ba abinki ba yanzu ai ba'a wannan kasadar, mace itace uwar ya'ya, itafa ba zata siyar da gida ba yayanta na ciki, shi yasa fa ake fada maku ku daina makahon so dan idan kuka ringa mika mana kudadenku da yan kadaririnku mun ga damar a kan gardama mu batar da su a dawo a shiga uku, shi yasa na saka sunnan maman yarinyar dan kar a je a dawo mijin ya siyar da gidan, sannan ke in banda abinki in kyautar abinda kike tunani ne ai ba dai wannan gidan ba, dan gaskiya na raina shi wa FATIMA, sai dai wancen gidan na nan gaba kadan , kuma da kuke cewa abu ba zai taba yiwuwa ba lamarin na Ubangiji? Da na zama sarki gadon Ubana ne? Sai ki ga abu ya zo da karar kwana, Sarkin dogarai ya tafi, a cikinku ke ko daya ta tafi, kin ga sai in kawo Fadima malan, mata su ringa tafe maza na rakiya da ido, Allah dai ya sa da sauran karfin yin aikin da ya dace a jikin maza" Bata taba jin cin fuska da rikaken iskanci irin na yau ba, a matsayinta, da kimarta, da isarta, da kyanta mijinta ya ringa magana irin wannan a gaban idannuwanta? Ashe haka abin yake da ciwo? Idan zata tuna shekarun baya da ta hada matansa da lalurar rashin anfanarsa a saman bed a gaban idannuwansu yake kodata da mata kirarin da sai dai ta ga sun sada kai, ashe haka abin yake? Mikewa ta yi tana gyara alkyabarta, domin ba zata iya ci gaba da maganar nan a yanzu ba, Har ta juya ta jiyo muryarsa yana fadin" Ki tabatar WA'INDA zasu bata kula dan gyaran mu'amalarta sun iya kuma sun iya rike bakinsu, gyaran amaryarnan da ake yi ai ita yar nan inaga bama ta bukata, yarinya da ace a gidan hutu ta tashi har an shiga uku da kallonta, ni da kaina saura kirissss nace alfarma aka yi masa yaron cen!" Zuba masa ido ta yi, gashi dai shekarunma sun ja fa, ama tatacen iya shege a gindin bawan Allahn nan, Murmushi ta karkaro mai daci a ranta ta ayana' Lalle baka san kaidin mace ba, da ka wulakantani da kula baiwarka ko a dadironka ce gwara na kumsa maka shinkafar bera ka ci ka kumbura ka fashe a dakinka, dan walahi mutuwarma ba zan bari ka yi mai daraja ba tsohon najadu!, Gida kuwa karya kake ka ba wata katuwa yata a raye a zaune ita ta tashi a banzar bazara kennan?" A bayane kuwa sai ta yi murmushi ta ce" Du ka rikice Aban BAHIJA, bayan baiwa sunnanta baiwa" Murmushi ya yi yana janyo abincinsa ya ce" Hakane, sai dai wata baiwar cike take da BAIWA, abin saima an dangana da room din ciki" Da sauri ta yi gaba, ta fahimci yau banda yan wulakancin harda yan iskan ke kansa Tana zuwa bangarenta ta saka aka mata kiran masu gyaran jiki da lamura na gidan sarauta, bata haye bangarenta ba sai da ta ja masu rikaken warning ta kuma sheda masu aiki tukuru, kar su ringa hutawa sai na cin abinci ko yin sallah idan sunna yi, kar su barta ta huta sai sun gamsu da yannayinta, gyara na waje kadai ba sai sun yi mata na ciki ba domin ba bukata, sannan su iya bakinsu, sai nan da kwana goma za'a dauko su Tana shiga sama ta bude whatsup dinta ta masa magana a kan matansa da kuma ya'yansa, sosai ta tuna masa me suke son boyewa sannan ta sheda masa cewa ya yi da gaske idanma ba hali kawai ya fitar da su waje, sannan ta kashe ta ringa kai kawo zuciyarta na mata daci, da gaske fa magangannunsa sun mata zafi fiye da tunanin bawa, haka kuma maganar gidan nan ta daga mata hankali, sai dai ba komai zata bi abin yadda ya dace, idan ya yi wasa sai ya wayi gari ya ga wata gagarar ta gagareshi! ( Ku dai kuka sani ku kashe kanku ) ________________________ *AGADAZ* Lulumin da aka wuni da shi jiya har aka kwana da shi wayewar yau ya saka yawancin jama'ar garin hutawa, idan har ba aiki nw da kai a cikin masarauta ba to fa kana hutawa ne, domin sanyin garin ya hadu ya bada wani irin sansanyan ni'ima mai tada tsumin mai mata, ya rikita gwauro A irin wannan lokacin, a cen cikin dakinsa ya gaji da murmususun tashin hankalin dake jikinsa ya mike cikin nutsuwa ya watsa ruwa sannan ya sha lipton mai zafi ya saka sasaukar sutura ya fito daga dakinsa yana duban agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa yana tunanin Anya yau zai samu zaman da yakan yi da Auta kuwa? Ya tabata itama tana cen daki ta labe dan bata son sanyi, gashi irin ranakun nan da baya fira fada, baya amsar korafin kowa yake samun zama da ita su yi hira da wasa da dariya Karar TV ya saka shi dakawara daga sama ya dubi kasan dan gannin wa yake kallon a falonsa? Ya tabata ba zai wuce cikin mutun ukun nan ba, dan su kadai sukeda wannan damar a masarautar, ta shigowa Falon nan kansu tsaye Ido ya dan zarro gannin abinda yake hange, watau su ukun ne gaba dayansu a zaune a falon, harda su TV? Ikon Allah Kasancewar jalabiya ce mai ruwan milk colar a jikinsa sai dan ta karra haska farar fatarsa sabbaj ta lafe a jikinsa kadan har ana iya gannin farar rigar dake ciki da kuma wandon rigar da bai idasa masa har cen idon kafa ba A nutse ya idasa saukowa, dukkan hankalinsa akansu , a lokaci daya kuma Umma da matarsa suka mike dan girmama shi da yi masa barka fa saukowa, Auta kuwa ta sauke ajiyar zuciya murmushi na wanzuwa a saman fuskarta ta dago daga rubutun da take yi da larabci tana kallonsa A tausashe ya amsa gaisuwarsu da murmushi kawatace sannan ya zauna a kujerar da take tasa ce, dama babu wanda ya hauta yana duban Umma cikin fitar haruma kamilalu ya ce" kin jima a nan ba Umma?" Umma ta yi murmushi tana kallon Matarsa da ta dawo dauke da abin sha mai sanyaya zuciya ta tabe bakinta a boye sannan ta budi bakin tana kallonsa ta ce" Ban jima sosai ba Yarona, ai ko wuni na yi ba zan gajiya ba tunda magana ce da ta shake ka, ka ga kuwa dole na bada hankalina dan gannin na tsaya tsayin daka a kan komai" Kopin ya amsa dauke da jus na Tataciyar Kankana uwar ruwa ba siga sai madarar peak da aka kwalala ta zamo mahadin markaden kankannar ya sakar mata murmushi a saman lebensa ya furta" Allah ya maki albarka" Murmushin ta mayar masa itama tana jin wannan Adu'a har kasan zuciyarta sannan ta mayar ta sake dawowa ya zauna a daf da kafafuwansa ba ruwanta da wata Umma bale Auta da sam hakan ba damuwarta bane ta kamo kafarsa ta dama ya dora a saman cinyarta dake dauke da tufafi fati irin shigar mata, watau lesh mai tsarin kwaliya fa kyau a hankali ta shiga dan mamatsa masa yatsunsa wanda hakan ya saka shi dan sake kureta da ido sannan ya dauke dubansa a hankali ya maida kan Umma da mamaki ya kusan kasheta da tunanin lalle tana sake fa da yarinyar nan, itace har ta samu damar taba kafar ASADEEK? lalle wannan din wani shinfida ne dake nuna mata cewa gaba ana iya zarce haka Lebe ta dantse a ranta ta ayana' Sakarya, babu anfanin haihuwa ama sarauta da kudi sun zaunar da ke shekara tara, haka zaki kare in dai ba zaki tafi ba, barama na cusa maki bakin ciki' A bayane kuwa ta ce" Dangane da maganar sadakin da ka ce Bafanka zai biya ne na zo mu sake yin maganar sannan mu tatauna a kan maganar yan zuwa daurin aure da komai da komai, ka san aurenka ake magana, ya zama wajibi a sheda" Daga shi din, har Matarsa da Auta dagowa suka yi suka zuba mata ido Bama matarsa da ta dan dakatar da murza kafarsa da take yi ta zubawa Umma ido gabanta na dukkan uku uku A hankali ya janye dubansa, a ransa yana ayana' me kennan wannan Umma ta yi? Kai tsayen nan zata fitar da maganar nan a gaban HUZNAH? Koda ya mata hirar ya dace a fan ringa kiyaye idannuwanta, ba dan komai ba sai dan a daraja hakurinta da kawaicinta' A fili kuwa sai ya dauke duban nasa a tausashe ya dora saman fuskar HUZNAH Umma ta ci gaba da fadin " Ita din y'arsa ce, idan har ka ce ya biya sadaki ai ba'a mutunta ba yarona, ya dace mu kai sadakinmu, sannan mu ware yan zuwa daurin aure da yan dauko amaryar ko?" Idannuwansa ya lumshe wannan karron, a sanyaye ya sake duban Auta da gaba daya ta daina dukkan abinda take yi tana kallonsu su dukansu Dan murmushi ya sakar mata kasa kasa ya ce" UMMA, idan lokacin ya yi zaku tafi da sadakin......., Ama bana son gangami domin bana bukatar hakan" Umma ta sake dubansa ta ce" Ba zaka je daurin auren ba kai yarona?" ASADEEK ya dubeta da dan mamaki, Shi? Kai yau fa Umma gaba daya sai wani abu take yi bako a wajensa, to me ya hada shi da zuwa daurin aure shi kuwa bayan tarin abinda yake gabansa? A yanzu haka shari'ar da zai zauna a gobe ta manyan sojoji uku ne, an kashe daya a cikinsu kotu ta turo masa dan ya yi tsakani sannan su koma kotu a dora da shari'ar domin so ake yi idan har aka gane waye makashin a zartar da hukuncin bisa shari'ar musulunci, dan abin na neman ya zamto ruwan dare, sai kuma kawai ya tashi ya je wani shirmen auren da suka hada? Shi fa wasu abubuwa ne yake tunanin zai samu daga yarinyar ya sa zai amince, ko meye ai mataki ne na gane sirrin dake birne mai mahinmanci! Kai ya dan girgiza bai ce komai ba Cike da kissa, Umma ta ce" To shikenan, in sha Allah hakan za'a yi yarona, bara na je na ga me ake yi a bangaren madafa, yau kana gida bana so a maka abinda ba zaka iya ci ba" Da ido kawai ya iya raka Ummar, wani lokacin mata kam na abubuwa a duniya na kai sake, sai dai hakuri kawai A hankali HUZNAH ta sauke kafarsa daga saman cinyarta ta mike a nutse ba da kwaramniya ba ta nufi hanyar fita ba tare da tace komai ba Muryar Auta a ba zata ta saka HUZNAH dakatawa da juyowa ta kalleta, haka shima da sauri ya kalli Autar yana son fahimtarta, domin sunnan HUZNAR kawai ta kama sannan ta mike ta ajiye kayan rubutunta a nan ta fice ba tare da ta ce komai ba Ido ya dan kifta yana cike da tunanin kennan Auta kan gane wasu abubuwan wasu lokutan? To in ba ta gane ba'a kyautawa HUZNAH ba bai fahimci reaction dinta ba, bayan ba wani shiga harkar junna suke yi da Huznar ba, ama kuma basa fada ko gaba, kawai ba ruwan kowa da kowa ne, kowa ta kansa yake yi Kai ya cira ya mayar kan Huznah Hawayen dake saman kuncinta ya saka shi zuba mata ido yana kallonta A hankali ta dawo ta zauna a saman kujera tana fuskantarsa muryarta a dan rikice ta ce" Aure zaka yi ?" Gefensa, watau daf da shi ya mata nuni da idannuwansa, dan haka ta karaso ta zauna tana sake zubawa kasa ido Shima nazartarta kawai yake yi har sai da ta tsargu ta dake dubansa Murmushi ya sakar mata kasa kasa ya ce" Wai ba, aure zan yi, suka ce saura kwana 12 yau" Idannuwanta ta rintse sosai, domin bata taba tunanin a irin yadda rayuwa take ita da shi dan ta ji irin haka zai iya daga mata hankali ba, sai dai ku gane, koda auren hadi ne, koda babu wani abu da ya mashe su guda, shi din mijinta ne, abin alfaharinta, kuma ya isa a yi kishin nasa, dan haka ba zata ji haushin kanta ba dan ta ji kishin abinta, kawai dai ta ga ta yi garaje ne, bayan ta san menene gidan sarauta tunda itama daga ciki ta fito, ko a gidansu daki hudun nan na matan mahaifinta mata ne nasa yare daban daban Sunnayen Allah ta yi ta ambata a cen kasan zuciyarta, hakan ya sa ta samu kwarin gwuiwar kamanta halaya irin na matan zamanin da ya shude A sanyaye ta furta" Allah ya sa hakan shine alkhairi a garemu baki daya, Allah ya sa idan ta shigo ta kasance mabudar warwarewar abinda yake cikin duhu ko menene a cikin Fadarka UMUGHLUK ITIFAL" Ya ilahi Manzan tsira, bai taba tunanin haka ne zai fito daga bakinta ba, duda ya shiryawa tarota tsaf, sai gaba daya ta saka shi zuba mata ido yana kallo kamar bakuwar Halita, ga dai yannayinta hankalinta ya tashi ainun, ga yannayin zamanta abinda ya fi karfi a auren bats samu, domin rashin samun sex shine babar matsalar lalacewar aure da kuma rashin samun care daga wajensa, banda hirar baki yana kiyayewa dukkan abinda zai hada jikinsa da nata, dan jikinsa na amsawa, ya murde tamkar karfe, idan ya zo a haukace sai ta koma ta langwabe, ya yi kwana da kwanaki yana jinyar kansa, da bacin rai da komai, shi yasa kawai ya dangana sannan ya bata damar salamarta ko zata rayu irin rayuwar farin ciki? Ama firrr ta kiya ta nuna zata zauna da shi a haka, bayan ya san koda yaushe tana iya gazawa, dan Adam take ai ba cikin jinsin da Allah bai halitawa bukata ba, wannan yannayi kuwa ya fi kowa sanninsa da zafinsa A hankali ya kamo hannayenta ya janyota jikinsa a ba zata ya rungumeta a cikin kirjinsa ya dora hancinsa a saman gashin kanta da ya ture dan kwalin da kansa ya lumshe idannuwansa yana shinshina Ya Allah ga mace fa, har mace, bafilatana mai kawaici da nutsuwa, halalinsa mai kanshi, wace da ace yanada lara bulaleta zai wanzar da rayuwa irin ta mafarki da ita, burinsa da iyalinsa idan suka rufe a bangarensa ko nata har tsere su yi, burinsa mace ta ringa masa yawo a ita dinta yana kallo, shi so ya yi zumuntarsa da matarsa ya kasance ko anguwa ta je idan ta tuna ta zabura sannan ta saki murmushi, a tsarinsa zasu kadance aminan junna, mashawartan junna , kawaye, kuma yaya da kanwa, zasu rayu cike da adinni da koyi da manzon Allah Sallallahu alaihi Wa salam, sai dai kashhhh duka kaf katangar nan na masa tsayuwar giginya tsakaninsa da ita,domin ko yaya ya so sakewa yanzu gwaurancinsa zai zake ya haifar masa da ciwo, ama kuma ko menene ya kaima Allah kukansa, ya san zai samu sauki yau ko gobe, ama ba wai ta karrin aure ba, aurenma BAHIJA yarinyar da ya ji kallonta kadai na neman saka shi amai dan ta yi abubuwa kusan uku da suka saka ya sarewa ƴaƴan yanzu har yake dubanta da wawuya wace ta bari shedan ya yi tasiri a kanta! A hankali ya furta " Kar hakan ya dameki MATAR ASADEEK, ke kin san sunna ne babu wani tasiri a tafiyar" Idannuwanta ta dago a hankali tana kallon pink lebonsa, sannan tana shakar sansanyan turarensa ta ce" Ni kuwa zan damu,domin ina kishin mijina.........., Kuma tasirin nan da muke nema muna barar mu wayi gari mu ga cewa ya tabata" Tabas hikimar iya hira da mijima abu ne mai kyau, murmushi ya sakar mata yana dubanta ya rike habarta a hankali ya ce" Menene abinda ya dace a yi wanda zai sanyaya zuciyar mai ASADEEK?" Ya Allah kamar ta daka tsale dan murna haka take ji, dan wana idannuwanta ta yi tana kafe lebensa da kallo, kasa kasa ta ce" Ana iya yin sharar fage da rarashi irin na uwar gida, sannan a goya ni, harfa da su kishin laifi ake yiwa mata, irin na dira na yi ta ihu kana rikonin nan ur excellency" Murmushin da bai shirya ba harda dafe haba ya yi yana wara manyan idannuwansa madu launin ja kadan ya ce" To fah, ke da ba mai shigar jinnu ba HUZNAH? Rada min a kunnena zaki rakani zuwa shan ice cream da dare a fitar sirri?" Da dariya a fiskarta ta ringa gyada masa kai sannan ta dora kanta a saman kirjinsa ta kwontar tana jin yau tamkar wata gagarumar sallah ce a wajenta, rana mai daraja ce ainun a wajenta, sai take jin kama zata summe dan dadi.......................................................................... ( Lalle zaku shiga uku, watau rayuwa sak irin ta an gayu abinku , laushi ruwan sanyi😁 bayan ga mata tafe🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ oh) ___________________________________ A TANUT A cen cikin dakin da aka ware dan gyaran amarya a yau rana ta uku da tsayuwar zancen da ita mai tafiyar bata san da shi ba, sai a yau mahaifiyarta ta shirya tunkararta tunda a kulun idan za'a je wannan bangare na koyon abubuwan da ake koya mata sai an zarre mata ido take tafiya, domin bata ga anfanin tafiyar ba, bata san ma'anar yin hakan ba! Daga ita sai tawul fari a daure a kirjinta, wanda ya rikide ya koma kalar yelow dan abinda ke mulke da jikinta, ta rike shi tsaf tana harare harare , a cen kasan zuciyarta kuwa cike da tunani kamar kanta zai fashe dan rashin amsa HINDU ce ta yi salama tana kallon Buzayen dake zaune wa'inda hausar kirki basuda ita ta yi dan murmushi tana sake rike abinda yake hannunta da kyau tana boye shi ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 1️⃣7️⃣ Tana boye abin hannunta da kyau da yaren hausa ta dube su tana daga masu hannunta tana murmushi ta ce" Yan kundun uba ana aikin ko?" Dariya ce ta kwacewa NADIRAH wace ta hada gabas da yama tana aika masu harara, domin aiki ne suke yi mata mai masifar zafi, gashi ko magana sai wani iri suke yi mata sai su ce muryarta tana tashi sama a dole sai ta tausasa muryarta kuma sai tana yi tana ajiye dubanta tana hutawa ba dan ta gaji ba, ta rasa wannan masifa da me ta yi kama, jama'a burinta su fece da innarta su tafi kauye, itafa lamarin birni nema take gannin an cika fariya, wai ace yau a gidan nan innarta abinci kala biyu take yi safe daban dare daban? Kala biyu fa jama'a kuma da kunduma kunduman nama a ciki, an tatso nono an saka a wai shi friza an shake, yar iska ce ita zata sha kankara sanyi ya kamata? Ai innarta na zuwa ta tatso mata mai dumi walahi, ya fi tsaki ai, gaba daya sai a mikota gaban matan nan da magana ke masu wahala ace su shafa mata kayan shafe shafe irin na yan gayun da suka gagari iyayensu, yo suka gagari iyayensu mana, abinda a kauye ana fada cewa mai shafa abin nan dan ya yi ja dan iska ne? Abu dai sai karra yawa yake yi sai Adu'a kawai kuma Abanta na kallo? Gida an saka karti biyu na gadi babu mai fita sai innarta sai Abanta, umantama bata zuwa ko'ina bale ita rabonta fa rana ta kwali fatar jikinta kwana biyu kennan, sai dai ta hangi rana , rana ta hangeta, idan ta tuna wannan abun hankalinta kan tashi, bama idan ta tuna wani shegen laushi da fatarta ta fara yi da wani kanshi da take fitarwa sai ta ji ta sarewa duniyar, yau idan ta koma LABA aminu yace ta zama yar iska ba shi ba ita fa ina ake so ta saka ranta? Dama innarsa ta san sai gyaran Allah, dan tana iya cewa ta zama yar iska ta haramta aurensu da Aminu bayan ita da Aminu sai balbalin balaki ne kawai zai iya rabasu da junna HINDU itama tana yar dariyar kasa kasa ta sake duban NADIRAH da hausa dai ta ce" Ki daina dariya da karfi kar su koreni su ce sunna aiki ina mayar da su baya mana yar gudaliyata" Sai kuma ta koma yaren buzanci ta dube su ta ce" Barkarku da aiki, gaskiya kun iya aiki , Allah dai ya karra girma" Amsa a wani yangance ta samu, ita dai ba shine a gabanta ba, abinda ta dawo da shi ta karasa ta yi zaman kaka gida ta basu baya ta saka y'arta a gaba ta ciro leda biyu ne , dayan a cikin galan dan karami, dayan kuwa a kule a leda guda ta girgiza ta bude ta ce" Maza maude ki bani galan din da shi zan koma gobe in sha Allahu" Abin take kallo, sai ta kalli Innarta ta ce" Inna, shima maganin zahin ne?" Innarta ta harareta ta ce " Ni wai Indi a me kika daukeni ne ni? Ya du idan na miko maki abu sai kin tsatsareni da tambayoyi kamar wace zan saka maki susau a ciki? Kin maude ko sai na moda maki mari?" Da sauri ta kafa ta rintse ido a tunaninta wani dabri dabri zata ji, ko kaifin wani abin, sai ta ji rubutu ne babu dabri babu kaifi sai kanshin tawada da irin kanshin rubutun nan, dan haka ta shanye shi tassss, ta miko hannu ta amshi na ledar shima ta tila ta kafa a bakinta ta shanye shi tassss tana murmushi ta ce " Innata wannan ai rubutu ne dama kin saba bani walahaula a gida ai, na zata wancen abin ne maganin zafi ko me? Ki ga fa wanda kike sakani tsakiyar dare, innata sai na yi barci ba gaba ba baya barci ya yi masifar dadin nan kike sungumata ki tsomani wai dan kanoma da bakin duniya, Innata ki duba ki gani kika wuni kina rubuta yusufa kika wanken na sha wai meye ake yi dan Allah?" Hindu ta yi tsuru tsuru zata bata amsa mai murzartar nan ta taso da hadi na kwai , da sauro Hindu ta boye abubuwan da ta shigo da su tana watsa mata hakora Matar ta sakata mikewa ta dubi Hindu ta ce" Ki koma ciki, zan mata wankan madara" Hindu ta yi wata yar dukawa ta ce" Yanzu kuwa hajia, Yar gidan Inna sai na kawo maki maganin zafin zan fada maki, ai zafi ke rarakarki yar albarka sai na dawo" Kamar ta bi innarta haka take ji, wai wankan madara, wannan abuma na kona mata rai, ruwan madara da ake sha a yi kat ita dumamashi ake yi a masa hadin su zuma da duminsa a sakata ciki a dora mata kokomba a gurmin idannuwanta a lafta mata hadin kwai da nescafe da madara a fuska a mata gargadin banda magana ko dariya kar ta bata fasalin fuskarta? Ai ita take kan gannin rayuwa , tsakninta da su bata san ba sai ta hada su da Allah ko ba sai ta yi ba? Ta dai zubawa sarautar Allah ido HINDU na komawa ciki ta tarar da Fadime ta gama girki tuni tana gyara komai , falon kansa yana fitar da dadadan kanshi ta zauna saman kujera tana fadin " Ya arahamani ya rahimi Allah mai gabas da yama, kudu da arewa, mai tudu d gangare na gode maka da ka dawo da ni lafiya ka saukoni daga saman jaki a cikin kasar sahara" Fadime ta sake juyowa da mamaki tana kallonta, ruwan da ta yi niyar daukowa ta dauko ta zo kusa da ita ta zauna tana kallonta ta ce" Yanzu tsakaninki da Allaj daga Timiya kike HINDU? Me yasa bakya jin magana ne ? Yanzu da ake tarewar nan da aka tareku fa? Kariya ba tana Adu'a ba muma kuma muna yi? Haba HINDU" HINDU ta dauki ruwan sanyin nan ta sha ya isheta ta ajiye tana yin mika ta gajiya ta ce" Aunty tunda na dawo ai shikenan, ama aunty na ga ikon Allah,malamai irin namu masu tsoron Allah, ba malaman tsubu ba, Aunty tsaf aka rubuce wakadimna kafa dubu arba'in da daya aka bani na wanke da dan ruwa kadan , sannan aka rubucen wasu na tsarin aka wanken na kamo hanya, kin ga harda tsuminsu na kauye na matan sarakansu aka bani, ai ni tafiya ta yi kyau sai hamdallah kawai, nema kuwa du abinda akace in ba Indi zan bata ne, Allah ya kama mana ya tsareta" Haba ta rike tana kallonta ta ce" To ina rubutun yake?" Hindu ta dubeta tana murmushi ta ce" Haba ke kuwa, a saman jaki fa ana tafe rike nake da galan din ba da igiyarsa ba, yaya zan yi wasa ai fatana na shigo gidan nan, ina shigowa na bata ta shanye tasss, Aunty yaya maganar ruwan zigalan kin saka min a frij din?" Fadime ta sauke ajiyar zuciya tana jinjina kai ta ce" Na saka, na zuba peak dinma a ciki, sannan na markada maki kankanar itama, kuma na markada cocumbar da peak din, tunda kin riga kin saka kanki a tunanin da bashida wani tsari ai sai ki yi, ni dai ido ne nawa, kuma in sha Allah yau zan mata bayanin nan, tambaye tambayenta sun isheni gaskiya" A firgice Hindu ta mike zaune daga ringesawar da ta yi ta yi wiki wiki da ido ta ce" Yau yau Aunty?" Fadime ta gyada kanta Hindu ta ce" Ama me yasa yau?" FADIME ta dubeta da kyau ta ce" Kamar yaya me yasa yau? A irgenki yau saura kwana nawa igiyar aure ta hau kanta?" HINDU ta sake yin wani iri ta ce" To ama, me zai hanna ki bari in je gida sai ki sanar mata?" Fadime ta girgiza kanta ta ce" kin ga ki daina irin wannan sarewar, kar ki saki ko nuna gazawarki a gabanta walahi, kuma da kike cewa ki je gida ya dawo daga tafiyar ne?" HINDU ta ce " Aunty dan Allah kar ki yi maganar nan yau, walahi rikitamu zaki yi, karma ki mata maganar nan" Fadime ta mike tana tabe baki ta ce" Ai sai ki yi,ke da kin san da mi za'a shiryata ama kike haka? Ya dace tunda wuri ta san abinda ke jiranta ba sai lokaci ya kure mana ba, domin bamu san lokacin da zasu dauketa ba, su kuma kwaliyar kawai zasu koya mata sai mugun nufin" A haka HINDU ta idasa wuni a ranar, sukuku da ita tamkar bata da lakkah, sai idan lokacin cin abincin ya yi ta je ta kai mata madarar da dan abinci kadan sai kuma wani hadin cikin dubunnan hade haden da take bata na gyara, tun daga na sanhi har na gyaran mata, ita babu ruwanta da wani wai ga yadda mijinta yake, wannan su ta shafa, ko wace wace kawai Aban NADIRAH na dawowa shima da Innar birni ta sheda masa a yau fa zata fuslanci NADIRAH da amsar tambayarta domin kwata kwata ta hannata sakat, in me take sai ta tsareta da tambayoyi, tana tambayarta gidan nan fa? Wa ke basu abincin nan? Yaushe zadu tafi? Me yasa ake mata wannan abin? Na menene? Ita bata so dai da sauransu Shima jikinsa sukukun ya yi har yama ya yi sosai aka dawo da ita aka kuma shige da ita aka yi mata wanka da turaren ruwa a cikin ruwan wankan sannan aka bata sutura mai dumama jiki da su safa aka umarceta sakawa bayan an shafa mata mayukan gyaram kafa da su tafin hannu Zaunawa ta yi saman babar kujera a falonsu tana girgiza kai, gajiya na tare da ita tilis ama magariba ta shigo ba danar yin barci yanzu, Innar birni na kusa ba zata bari ba, innarta kuwa tana daki wai nafila zata yi, ko sallar magariba ba'a yi ba a gaba ama innarta ta shige nafila, ko ta mecece? Yannayin zamanta matar nan ta yi tsaye a kanta tana mata fadansa, ta fuskanceta da kyau ta ce" N hannaki zama irin wannan, wannan din ba zamanki bane, ya dace ki ringa zama irin na masu matsayinki, daga yannayin zamanki ne jikinki zai dauki yannayin tafiyarki, kin ga fa kanki, da idannuwanki komai zaki yi da su ne, idn ba ke da makusantanki ba babu wanda zai samu yawan maganarki, ki gyara zamanki ko mu yi gyaran dare yau!" Da sauri NADIRAH dake hararen gefe ta zarro ido ta juyo tana gyara doguwar rigar dake jikinta ta gyara dan kwalinta da kyau sannan ta gyaran zamanta, ba zama irin na kafa daya kan daya ba, no, zama irin na hade kafafuwa wahe daya sannan a basu karfi gefen hagu ko na dama, haka kuma bayanka kan bada yannayin halitarsa da kyau, kuma dukkan wani fasali naka kan fitowa da kyau da irin girman isar da sakon yannayi a irin zaman Ido ta zubawa NADIRAH, har yanzu takan ji a rants yarinyar kamar ba Yar bayi ba, koda yake ko menene ta tabata mai girma le tunkarar rayuwarta Idannuwanta na matukar bata mamaki, kamar ba yar africa ba?, Yannayinta na bata mamaki, mutun ce mai son sakewa, Dan murmushi ta yi a boye, kasa kasa ta ce" Ki dan saki fuskar taki, ki kasance mai aika murmushi koda ranki ya bace ba fushi ba kin ji?" NADIRAH ta gyada kai, tana kallon matar ta juya ta fice cike da takama hakan ya sa ta rakata da harara har kamar idannuwanta zasu fado kasa dan rigima Innar birni ta sauke ajiyar zuciya, a hankali ta ce" Hararanta kike yi?" A zabure ta juyo tana daidaita yannayinta, kasa kasa ta yadda ita da kanta bata san cewa abinda take gujewa ya fara tasiri a kanta ba ta ce" Aa innar birni, bara na je na yi sallah" Kai Fadime ta gyada a hankali ta ce" Idan kin gama, ki same mu a dakin Abanki" Dan juyowa ta yi, sai kuma ta amsa ta shige nata dakin da har yanzu take mamakinsa, waje aljanar duniya ace nata ne? Birni birni basa jin tsoron Allah sam! _________________________________ Bayan sallar Magariba da isha'i Zaune suke su ukun , kowane ba yalwataciyar fara'a a saman fuskarsa, dama dama Innar Birni tana dan shan shayi ne a kofi irin na bugaje tana dan kallon su a ranta kuwa tana adu'ar Allah ya kawo masu koma menene da sauki Tun kafin ta shigo, samsanyan, rikitacen kanshi ne ya fara shigowa, sai da ta tsaya bayan ta yi salama har aka amsata sannan ta shigo da tafiar da ita bata san ta shiga jikinta ba , a tunaninta yadda ta saba ne take yi, sai dai daga Mahaifiyarta, da mahaifinta, da kanwar mahaifiyarta ido suka zuba mata dan abinda ya shiga jikinta abin girmamawa ne su a wajensu Zama ta yi daf da Innarta tana sake kallonsu da son gane abinda yake faruwa, Da sauri HINDU ta mike tana fadin" Bara na je falo na dan dakata, zagayawa zan yi ina ga cikin nawa ke son hautsina min" Innar birni ta dubeta da kaifafun idannuwanta , fuskarta na daukan yannayi na ba wasa take yi ba, kuma ba zata bi abin da taushi ba ta ce" Ki zauna malama, bana son shashanci kin ji?" Mijinta ya sauke ajiyar zuciya kamar shi aka yiwa tsawar ya dan kura mata ido sannan ya maida dubansa kan Y'arsa da gaba daya ta zamto abin kallo a wajensa, kamar ba NADIRAH ba, dama yarinyar akoy ruwa irin na manyan mutane a tatare da ita, ama abin bai kai haka ba, a yanzu kwana uku kacal du kamar ba ita ba, akoy halayanta na da, ama kuma ta wani irin salo take sakinsu a yanzu HINDU zata ta yi ta sada kanta tana sauke ajiyar zuciya, hakan ya sa NADIRAH zubawa mahaifiyarta ido hankalinta na neman tashi Mamanta ta fuskanceta da kyau ta ce " NADIRAH, wannan zama da kika ga mun yi a nan, zamanki ne, mun zauna ne dan mu baki amsoshin tambayoyinki, sannan mun zauna ne dan mu yi magana ta fahimta wace zamu ganewa junna mu kuma dauki abinda zai tunkaromu da kyakyawar fahimta ko ma gudu tare mu tsira tare" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 1️⃣8️⃣ Hpy juma'at A sanyaye NADIRAH ta ce" Inna lafiya? Kamar wani abu ke faruwa?" Innar Birni ta sauke ajiyar zuciya, ta kalli mijinta a tsanake sannan ta sake duban NADIRAH ta ce" Eh wani abu yake shirin faruwa, wanda bamu da tabacin zai kasance din ko aa, idan ya kasance bamu san yaya zai bile ba, abinda muka sani shine abin mai hatsari ne, da kuma muguwar rikicewa, wace bamu isa mu saka ko mu hanna ba, ......Abanta, ko zaka taimaka ka bata tarihin iyayen gidanmu a kanmu? Ka kuma shaida mata alkhairan ZAKIN SARAKAI?" Zamansa ya gyara yana hadiyar yawu mai daci a wuyansa ya fuskanci NADIRAH a sanyaye ya ce" Tarihi ne ginane, tsohon iko ne da yake da tasiri tun a lokacin da ake yin mulkin kama karya, An yi zamani kala daban daban na sarakai masu iko daban daban a NIGAR, an yi zamanin sarkin dake yiwa budurwa cabe a jikin garu har sai ranta ya bar gangar jikinta, magana ne ce ta zamanin da da yanzu, magana ce ta mulki mai matukar daraja da wanda yake na kama karya, ko a shekarar da democradiya ta shigo mana a shekara ta 1960, ta zagaya ta yadu mun rike har bayi sun tashi daga dabobi sun zama masu darajar da har ake basu albashi na bauta, ama bawa sunnansa bawa kuma uban gidansa ya isa da shi a kan komai, saukin abin da muka samu a cikin sarakanmu akoy jajurtatu da duka giga har suka fi iyayensu karfi da tsayawa a kan gaskiyarsu, basa tsoron kowa ciki harda mutuwa, domin sun riga sun san cewa mutuwa da rayuwa hukunci ne na ubangiji, kuma lahira ce dawamamiya....Nadirah shin kina fahimtar abinda nake fada kuwa?" NADIRAH ta sake fuskantarsu, har wata zufa zufa ke neman tarun mata a goshi, dan tsakaninta da wanda ranta ke hannunsa bata san dalilin da ya sa iyayenta sakata a gaba ita NADIRAH suke dauko mata wata magana kamar ta aljannu ba, yo ita me ya shafeta? Ita ba baiwar kowa bace gaskiya, kuma ita kam harkar sarkakiya irin ta sarauta sam bata sonta, magangannunsu kulun a cakule basu da abu a bayane, ita kam ina ta ga hankalin gane maganar Abanta? A hankali ta girgiza kanta ta ce" Abana, gaba daya ni ban san me yasa ake maganar nan bama" "Abinda ake son nuna maki, karfi, da ikon da Sarki yake da shi a kan bawansa, koda an shigo zamani na yancin kai akoy abubuwan da suke da karfi da tasirin da yancin kai ba zai goge ba, bale idan ba haramun bane, Abinda ake son sake nuna maki shine sarauta da kike dauka makiyiyarki itace gatanki, domin Allah ya yi umarni da mu yiwa shuwagabaninmu biyaya, sannan a zamaninmu na yanzu munna cikin zamani da ya kasu kalla biyu ne , a cikin tafiyarmu munna tare da rikitaciyar tafia wace ta hada adalin da yake adali a garemu da kuma adalin da yake adali a gare shi!, NADIRAH kin fahimci maganata?" Innar birni ta fada a kausashe, hakan ya saka Nadirah jin numfashinta na mata kadan a hancinta, a hankali ta dan ja gindinta da niyar matsawa kusa da innarta, sai dai bata idasa aikata hakan ba ta ga innar birni ta matso daf da ita ya kasance sun sakata a tsakiya A hankali ta kamo hannunta ta rike da kyau a cikin nata tana kallonta ta ce" A lokacin da mahaifiyata take raye,an yi rikicin da ya hadu fa shari irin na bayi, aka dora a kanta cewa lamari na zina ya shafeta, shi UMUGHLUK yana zartar da hukunci ne bisa hukuncin musulunci, an kaita an garkame har an saka ranar jefeta, ashe shi din ba wanda ke aiki da gadara bane, yana bincike ta kasa, mun gama fawalawa Allah komai mun kauracewa kowa aka wayi gari da sanyin safiya aka fitar da rakardar wanketa tas faga sharin nan, tun daga lokacin nake kallonsa da kallo mai girma a idannuwana, cikinmu irinmu mun fi a irga dake dauke da daraja mai girma tasa a kirjinsa, wadda bamu taba haduwa gamu gashi ba, ama kuma a kulun muna binsa da addu'a" "Inna me yake faruwa?" NADIRAH ta fada muryarta na mugun gargada tana kallon mahaifiyarta Innar birni ta ja numfashi ta ce" Abinda yake faruwa shine, kadara ce zata biyo ta kanki, ta yiwu fara ce ko baka, koma wacece ita kike iya dauka muguwa ko mai sauki ta yannayin fahimtarki, abinda yake faruwa shine hukuncin rayuwa dake zuwarwa bawa ne ya riskeki, watau babu bawan dake rayuwa d asalin yadda yake so, kowa da irin takun salon kadararsa, ko wanene!, Ba komai bawa ke nema ya samu ba, mun yarda da wannan, hakane ya kasance a kanki NADIRAH............" Yanzu kam har jikinta ya fara rawa, haka kuma sun fara bata tsoro, haba, gaske take jin wannan shorye shiryen da ake yi mata baya birgeta, kennan da lauje cikin nadi? A hankali HINDU ta ce" Aunty, dan Allah kar ki rikitata, ba a haka zata fahimci maganarki ba, Kim ga Indi dubeni nan kin ji?" Hindu ta fada tana juyo da NADIRAH, domin gani take yi wannan salo da auntynta ta dauka sam ba zai kaisu da ci ba, ba Nadairah kadai ba itam dake sauraronta jikinta rawa yake yi bale NADIRAH A tausashe ta kama hannunta tana kallonta ta ce" Kin sani cewa, wani lokacin abinda bawa ya nacewa a so ba shine alkhairinsa ba, da yawama soyayar ake kamar za'a cinye junna har a yiwa iyaye tabara, da zarar an shige gidan kuma a dawo kiyayar junna, tunda ba'a nemi zabin Allah ba ko?" NADIRAH ta ce" Innata, Aminu ya rasu ne?" Kai ta girgiza ta ce" Da ransa Indi" NADIRAH ta kalli abanta da innar birni ta ce" To menene? Ku fada min menene kun ji? Me yake faruwa ne? Kalli Innar birni kamar wace ke kuka ko?" HINDU ta karra hadiye nata kukan itama a hankali ta ce" Abinda yake faruwa shine, sun so bada yarsu aure wa UMUGHLUK ITIFAL dan ta je ta isar da bukatarsu na kawar da shi a doron duniya, sai ta kiya , kasancewar tanada damar hakan a wajensu, sai abin ya juye zuwa................" "Hindu" Aban NADIRAH ya fada a hankali yana katseta HINDU ta saki hannayen Nadirah ta sad kanta hawayenta suka bale A hankali ta juya wajen Abanta tana kallonsa Mahaifinta ya yi dan murmushi ya ce" kina ji?, Na amince da haka, innar birni ta amince da haka, dan baban abinda ya fi janmu amincewa da hakan shine tunaninmu zamu iya kare wani abun ta damar da Allah ya bamu, Gaskiyarsa da kare yancin talakawa ya siya masa makiya, barima ki ji NADIRAH, ina iya guduwa da ku, domin masu tsaron kofar cen su biyu babu abinda suka isa su yi, na tabata idan na shiga masarautar da ku na sanar masa abinda yake faruwa zai iya daukan mataki, sai dai tsorona shine , shin sunne kadai mafarautansa ko maciji zan kashe ban sare kansa ba?, Na karashe maki magana , a amincewar tamu mu din ba masoya zamu kasance a gaban idannuwansa ba, ta yiwu idan mun yi nauyin baki har muna iya samun mugun hukuncin da kawunnanmu ba zasu iya dauka ba....., Haka kuma cikin hatsarin da zaki je ana iya cin galaba a kanki, a haka duka muka amince NADIRAH muka salwantar da farin cikinmu, ba dan komai ba sai dan mu kamanta kyautatawa wanda yake kyautatawa bayin Allah " Irin kallon da NADIRAH ke binsa da shi, kamar tana son gane a fuskarsa me da me aka hada aka haliceta ne!, Muryarta na rawa ta ce" Aba , da me kuka amince?" "NADIRAH ke fa ba karamar yarinya bace, shekaru ashirin ba kwana ashirin bane, a birni ko a kauye kin isa ajiye ya'ya uku rass naki, abinda ake nufi shine an saka aurenki ke da UMUGHLUK ITIFAL nan da kwana goma sha biyu bi'izinillah, zaki je a matsayin yar sarkin garin nan, zaki je ki rayu a cen a matsayin matarsa, bisa umarninsu, sannan zasu biki da wani aiki wanda idan kika aikata ke da ubangijinki, watau kawar da shi a doron kasa!, Abinda mu muke maki nuni a nan kuwa shine, biyaya ta zame mana dole, itace abu ta farko da zamu yi a matsayinmu na wa'inda ke karkashinsu, muna iya bijirewa duda irin tarin alkawarin salwantar da rayuwarmu da suka yi, haka kuma muna iya guduwa wajen da za'a iya hukunta su, ama muka zabi amincewar dan mu kamanta kyautatawa wanda ke kyautatawa talaka, ta hanyar amincewa ba dan mulkinsa ko arzikinsa ba, zamu mika ki bayan mun gama fada maki cewa duk rintsi gwara a tsire ki da ki aikata abinda suke bukata, watau kashe UMUGHLUK ITIFAL!" Innalilahi wa inna ilaihi rajune, mahaifiyarta na magana ne, barin jikinta na ninkuwa ninkin ba ninkin, wanda ya tsoratar da su baki daya ama kuma ta ki dasa aya sai da ta kai karshen maganarta sannan ta dasa aya tana mai saka idannuwanta cikin na yarta wace girman idannuwanta suka karru , fuskarta har ta dauki ja dan rikicewa, haka kuma numfashinta ya wuce misali a irin gudun da yake yi, watau sama sama kamar zata bar duniya Da kyar ta iya juyo kanta da ya mata nauyi ta kalli mahaifinta, sai kuma ta kalli Innarta wace kukanta ke shiga kunnenta Tabas maganar nan ba wasa bace, tunda a yadda suka sakata a gaba suka yi mata da kukan Innarta kadai zai tabatar mata da ba maganar wasa a lamarin A hankali ta sake duban mahaifinta da ya jimke hannunta da karfi dan ya hannata barin jikin da take yi Idannuwanta na shigewa sunna budewa ta kalle shi , muryarta na rawa ta ce" Abannnnnn, abbannnnnnnah, kunna nufin nice za'a za'a yiwa aure da UMUGHLUK ITIFAL Na baban Garin Agadaz a matsayin wace zata je ta kashe shi?" Mahaifinta ya girgiza kai da sauri ya ce" Ba zaki kashe shi ba Nadirahna, idan kin je ba zaki kashe shi ba domin ke ba azaluma bace, ke ba makashiya bace....." "Abana , to ni ai ya mutun zan fi so Abana....., Abana ku ce min muna iya guduwa a yanzuma, domin ba zan taba iya kasancewa yadda ake so ba, Abana kun san da wanda nake so ko? Kuma kun son bana son rayuwar sarauta ko ta dakika guda ce ko?, Abana ku taimaka min ku ce min zabi gareni, dan zan iya ce maku ya mutun ba zai dameni ba da a kaini gidna sarauta!" Ta fada muryarta a mahaukacin raunane, hawaye na bale mata, haka kuma tana haki tan sakw kure fuskar mahaifinta d ido Hankali tashe mahaifiyarta ta ce" Kina nufin, gwara ki kashe shi da ki je aure gidansa?" A zabure ta zarro ido tana girgiza kanta, muryarta a raunane ta ce" Ba zan kashe shi ba, Innar birni da na kashe gwara a samu gawata, ina fata da na kashe gwara a wayi gari a samu gawata, ama idn ya mutun ni kam babu ruwana, innar birni ku ce min shikenan mu tatara mu koma LABA kun ji? In sha Allah ba zamu kuma dawowa birni bama kun ji inna?" Mahaifiyarta ta ja numfashin samun dan kwonciyar hankali, dan har ga Allah ta tsorata da farko Komawa ta yi ta jingina da jikin gado ta ce" Ki yi hakuri, ki mana biyaya, bana son jan magana ki je dakinki ki yi sallah ki fadawa Allah, idan har alkhairi ne Allah ya tabbatar, in ba alkhairi bane Allah ya kade ta hanyar da kowa zai ji dadin abin , ki tashi kawai ki tafi zamu sake zama gobe in sha Allah " Da mamaki Mahaifinta da Hindu ke kallon Innar birni, amaa ta hade fuska tama daina kallonsu Magana abanta ya so yi ama innar Birni ta bashi barin fuska ta kara hade fuska alamun bata son maganar Hindu ta sake kallon NADIRAH dake cicibawa jikinta gaba daya sai bari yake har kanta ba a daidaice yake ba, sai zabura take yi, kana kallonta zaka gane magana take son yi ama tana tsoron innar Birni Tana idasa mikewa ta juya zata fita sai ji suke dimmmmmmm ta dimu a kasa ba numfashi a tatare da ita A haukace suke rige rigen karasawa inda take Da tsawa mahaifinta ya tare hannun Innar Birni ya ce" Ki barta, kar ki tabata Fadima!, Ki barta haka kar ki idasa kashe min ita!, Dan ni ina sonta, ina son abina!, Ko menene bako yake a rayuwarta, idan kika yi duba da irin kulafurcinta da abin, kuma mun zo mata kai tsaye da abubuwan da a maganar gaskiya sun girmami tunaninta dole mu sasauta, na san idan bamu yi mata da gaske ba, ba zamu iya tankwasata ba, ama kuma komai yanada lokaci, a kan me tashi tsaye zaki fitar mata da komai kuma ki koreta? Ki tuna ke kika sab da rayuwar bauta ba ita ba, Fadimata ki tuna ke kika san irin haka ba ita ba, ita din bata rayu da haka ba, shi yaa bata zama inda muke , dan bata son ganninmu a yadda muke, shi yasa take tafiyarta a wajen da babu hasken lantarki, dan ta fi ganewa ta yi dire direnta a birni hankali kwonce da rikicin cikin gida!, A hankali zata shiga irin rayuwar nan ba tashi daya ba, so kike ta gujeki? So kike ta kulaceki? So kike abinfa muke so ta kiyaye dan kauna ta aikata dan kiyaya? Haba dan Allah, dan muna talakawa ba mahaukata muke ba Fadimata, sai da muka yarda cewa mun amince, idan baki amince ba a yanzuma ina iya fitar da mu, da mu saketa a birkice gwara mu gudu tare!, A kan me zaki ringa irin haka? Kin hanna innarta ta bita ta yadda ta saba binta, kin ce ba zata saurara ba, bayan na tabata da ita din ce ta mata hirar sai dai su sha koke kokensu zata dawo ta rarasheta!, Haba Zahrah da wane kike so na ji? Ke Hindu daukarta mu je dakinta, ke kuma kar na ga kafarki a nan!" Rai bace suka tafi suka barta a nan tana tsugune, a hankali ta silale ta hade kanta da gwuiwarta ta fashe da kuka tana kai hannunta daidai kirjinta ta jimke da karfi , muryarta cen ciki ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 1️⃣9️⃣ Ba edditing 😊😂 Muryarta cen ciki ta ce" Allah, kaine gatan bawa, mai kudi da talaka, sarki da bawa, Allah ga yarinyata nan, ka tankwasa min ita cikin ruwan sanyi, Allah kai ka fi kowa sannin irin halin da nake ciki, wannan daula da tunanin zamantowarta matar mutun mai daraja baya dadani da kasa, na fi tsoro da zulumi a cen kasan zuciyata, bana iya ci, bana iya sha , bana iya rintsawa, dan na san wacece yata, na kuma san zata kasance ne a filin da babu wargi, ya Ubangi ka mayar da bakin abu fari a tafiyar NADIRAH"............... (Amen innar birni) A saman gadon dakinta Hindu ta shinfideta, jikinta na rawa a amshi ruwan da Abanta ya miko ta gumtsa a bakinta ta fesawa NADIRAH fesawar farko a fuskarta Sai dai bata farka ba, hakan ya saka mahaifinta a rikice ya ce" Hindu ko ki dauketa mu tafi asibiti?, Hindu ta ki farkawa?" Kai ta girgiza da sauri ta sake gumtsa da karfi ta fesa mata, wannan karron kam ta farka a rikice, sannan tana nan rarume rarume Da sauri HINDU ta rukunkumeta a jikinta tana bubuga mata bayanta tana ambaton sunnanta da sanar mata cewa itace a tare da ita kar ta tayar da hankalinta Murya a raunane, cikin yaren kuka mai tsuma zuciya ta ce" Innata, innata mu yi tafiyarmu, innata mu tafi, innata bana sonsa, bana kaunarsa, kuma bana son maganar a sakani kashe mutun, innata mu yi tafiyarmu wajen Aminuna, mu tafi innata" Hankalin Abanta tashe ya ce" HINDU, tunda tace bata so ni kam na hakura, ki kimtsata zan fita na sama mana hanya, na hakura ba maganar yi mata tunda bata so, tayar da ita ki shiryata mu tafi!" NADIRAH ta dago da sauri tana riko hannun mahaifinta tana gyada kai harda alamun fara murmushi ta ce" Abana, toh, toh Abana, mu tafi, ba sai an wani shiryani ba, mu je Abana, mu je!" "Mu je ina?" HINDU ta fada da dan karfi sannan a kausashe tana kallonsu Aban NADIRAH ya dubeta ya ce" Mu tafi ko'inama, ko ina mu je mana HINDU?" HINDU ta girgiza kai da mamaki ta sake saka hannayenta ta zaunar da NADIRAH da take kokarin mikewa ama jikinta ba karfi A kausashe ta fuskanci Aban NADIRAH ta ce" Ai kuwa yaya idan ta haka ne zaka iya yin wani abu gwara ka je kawai dakinka ka sasanta da matar cen da ka baro, domin zan iya rantse maka da Allah soyayar da kake yiwa yarinyar nan bata kama farcen wace take yi mata ba!, Itafa ta haifeta, du kusancinka da ita ba kai ka yi dawainiya da cikinta ba, ba kai ke gagara barcin dare idan tana wutsil wutsil ba, ba kai ke yawo, rana, zafi, ruwa, sanyi da ita a bayanka ba, yaya du wahalar soyaya da zaka nuna nake fada maka ragagiya ce a kan wace take yiwa y'ar nan!, Kuma ta fi kowa sannin wacece yarinyar nan!, Wai bama wannan ba, kana nufin zaka je ka rike makogwaron masu tsaron kofar cen, idan Allah ya baka Sa'a a kansu ta yiwu ka kashe su ka kwashe mu ka nufi wajen UMUGHLUK ITIFAL da mu ko ka je wani kauyen da a kankanin lokaci za'a kwasomu a dawo da mu nan?, Yaya kana tunanin du yar tsamar da suke tsakanin su idan ya tsaya a gaban dansa maganarka zata yi tasiri ne bayan bakada huja bayananiya wace zata saka a dubeka? Sunna aiki da ilimi ne, ka san wani laifi za'a lankaya maka kai da mu baki daya? An kar da dubu a kan laifin da ba nasu ba, ko kana musu?, Kai da zaka tayamu yaki a kan haka? Kai da zaka sheda mata Aminu fa karya ce a cikin gaskiyarta, zuma ce mai dacin balaki? Yaron da mahaifiyarda ta saka mata karan tsana ina take tunanin zasu je? Aminu ba zai taba biyota ba dan za'a masa aure da wata dan iyayensa na gaba da ita, itama ta sani, idan sun a shirmen soyayarsu uwarsa na tsaye a tsakiya, itama ta sani, sau nawa tana cewa zasu gudu idan aka hanna masu junna? Dan ubansa ba kudin aurensa aka kai ba? Me yace mata? Ciwon yatsa yake yi yana gindin babarsa!, Kuma ya dace ne ka ce da ita mamanta ta yarda, kai ka yarda haihuwarta aka yi dole ta yi biyaya, idan har NADIRAH ta kai wajen da zata bijire luma ba sai mu janye mu zuba mata ido ba, Yaya bana cikin wannan tafiyar, lalle abin ya zo wani iri, an mata wani kwana kwana bayan ya dace ne mu fuskanceta, ni da take wajena nakan fada mata abu kai tsaye ne, sannan na nuna mata a adini ba haramun bane ko haramun ne, koda ta yi kuka zata dawo ta yi hakuri! Bata fa kai wajen da ba zamu iya tankwasata ba yaya, haba dan Allah!" Ta karashe babu ko digon hawaye a cikin idannuwanta sannan ta juya wajen NADIRAH da ta yi dif kamar ba ita ke rizgar Kuka ba ta fuslanceta ido cikin ido ta ce".NADIRAH tsaya ki ji, maganar da aka fada maki gaskiya ce, bamu yi labe labe da kame kame ba dan muna jin tsoronki, mun yi ne dan muna gudun tashin hankalinki da rikicewarki, ba bacin ranki ba!, Idan mu namu tashin hankalin ba komau bane a wajenki ki bijire ki fice ki tafi ga kofa nan, NADIRAH kar ki amince dan an ce za'a batar da mu, kar ki ce zaki amince dan farin cikinmu, domin hakan na iya sakawa a cin maki da wuri, ke hakan na iya sakawa a wayi gari ki amshi gubar da zaki kashe Sarkinmu!, Ki shiga uku a duniya sannan ki je kiyama ki hadu da ubangiji, NADIRAH ke baiwa ce ba kowa ba, le yarmu ce, mu kuma bayi!, Ba maganar kina sonshi ake ba, ba maganar kin tsane shi ake yi ba, magana ce ta damar da Allah ya baki ake yi, wace kina iya cenzata da izinin ubangiji!, Nadirah gaskiyar mahaifiyarki ke ba jaririya bace, ba kuma dai na maki dogon tarihi ba, ke ba kurma bace a wajen dandali, a cikin kauye, a wajen sarakan kauyenmu, a bakin samari da yan mata masu shiga birni kina jin wanene UMUGHLUK ITIFAL!, shi din Uba ne, kuma kimarsa ta fi kargi laban bakina!, Yanada daraja, dan mutunci ne, mai kishinki ne ke talaka, kina iya zaunawa ki yi nazari idan zaki zauna mu tatauna ta yadda zamu ci karfin makiyan UBAN GIDANMU mu tatauna, ba dan maganar soyaya ba, bamu kawota kusa ba!, Ki yi dan ceto ne, ki yi domin Allah, idan komai ya lafa ta yiwu yana iya sawake maki cikin ruwan sanyi , idan har Allah ya bamu nasara yana iya yi maki abinda kike buri, a yanzu kam bara muke, kuma Umarni muke baki, dan ki kasance mai biyaya a garemu ba a garesu ba!, Ta yadda zamu buga wasan biri da ayaba!, Babu makiyinki a nan, kar ki kuma manta abinda nake fada maki *BA KOMAI DA KAKE SO KAKE SAMU BA, BA'A TSANANTA KIYAYA KO SOYAYA, ADU'A ITACE MAKAMIN MUMUNI!*" Daga haka HINDU ta juya tana ficewa a dakin tamkar zata tashi sama ta nufi nata dakin ta bude ta shige a hankali itama ta silale ta saki kukan da ta rike da dukkan karfinta a gaban y'arta, kwarai da gaskiyar yayarta, basuda isashen lokacin da zasu tsaya wasa da NADIRAH, idan suka ce zasu tsaya har ta bada amanarta ta laluba da rarashi da nuna kauna da meye meye meye ko? Sunna ji sunna gani wankin hula zai kaisu dare, itace a kauye, ama ga dukkan alamu ta fi yaya sannin rikicin wasu marikitan!, Shi a tunaninsa zasu je lai tsaye su ga mutumen da shekaran jiya da kansa yace sai a jima ana son ganninsa ba'a samu ba su kai masa wannan magana mai kama da tatsuniya kai tsaye dan shine aljanin sannin abu da hawa kan abu ya yarda ya hukunta bafansa? Idanfa yana tare da wanda koda za'a gile kansa ba zai taba yarda da cewa yana iya masa karya ba ya daurewa bafan nasa? Idan a wajen yin binciken Bafansa ya juyar da komai ya hau kansu fa? Shikenan sun zama mararsa ilimi dan basu je boko suka nitsa ba ko? Lalle zasu nuna masu islamiya itace tushen komai, a cen ake koyar da komai, su kuwa yayan malamai ne ba iya Alkur'ani suka karanta ba, da izinin Allah zasu kai ga ci! Itafa dama a duka kaf rikicin tafiyar y'arta take ji, tunda ta ji yanzun ko? Zasu ci karfinta in sha Allah! Irin zaman da ta yi a saman gadon bayan fitar innarta dole ta baka tausayi Kamanin fuskarta kana kallo zaka gane a wani hali take Fuskarta ta yi jajajir haka idannuwanta sun yi jajajir A zaunen da take ji take yi tamkar duniyarta ce ta zo karshe a yau Tana kawo magangannun nan ne sala sala tana bajewa da irin yaren da zata gane Da ace iya innar birni ce abin ya tsaya da ta tabata da sauki, domin dama innar birni ba fai fushi ba Sai dai magangannun innarta sun sakata a halin ita ba mutuwa ba, ita ba rayuwa ba A irin zaman da ta yi Allah ne kadai ya san halin da take ciki Mahaifinta ya sake zama a gefenta, muryarsa a tausashe sosai ya fuskanceta ya ce" Nadirahna, ki yi hakuri, ki yi hakuri kin ji? Ki yi hakuri sannan ki fadawa Allah, abin nan fa kila wa kala ne, ba lalle bane ya tabata, idan muka fadawa Allah shine zai yi mana zabi, sannan kar ki saka maganar Aminu a ranki, Aminu namiji ne kamar duban sauran maza na duniya, a kanki ba zai kashe kansa ba ko ua bijirewa iyayensa, ki dauka hakan ne alkhairinki, domin koda innarki bata da gaskiya a wani wajen tanada a wani, mahaifiyarsa bata sonki NADIRAH, nima ba zan taba bashi yata ba, domin koda yar Allah bani ce ke ina son abina, kema yar gata ce, kuma ki sani idan auren nan ya tabata ba yana nufin zaki dawama a gidan sarautar bane, na san bakya ra'ayin rayuwar sarauta, idan har Allah ya bayanar da gaskiya Nadirahna zai gode mana sannan ya salameki salim alim kin ji? Ki kwontar da hankalinki dan Allah ki fuskanci abinda yake gabanki, domin yaki ne mai girman gaske, a fada mai tsaurin gaske kin ji?" Bata iya bashi amsa ba, ama irin yadda take kallonsa ya san tana jinsa, vai bar dakinta ba sai da ya shinfida mata darduma da carbi da alkur'ani sannan ya tafi ya daura alwallah shima ya fito falo da dardumarda ya fuskanci gabas, domin ya san a yau ba zai iya rintsawa ba ko yaya ya so rintsawar A bangaren NADIRAH kuwa, a lokacin da ta fuskanci kowa ya fitta daga dakin nan an barta daga ita sai halinta tamkar wace ta rasu aka kawo kabari ta karra saukowa kasa gaba dayanta daga saman gadon tana kallon kasa ta ringa auna komai dala dala, tun daga bayanan mahaufinta,na mahaifiyarta, na innarta, irin gidan da suke ciki, komai da komai sai ta samu kanta tamkar mai hauka sabon kamu Salayar da mahaifinta ya shinfida mata ba itace a gabanta ba a irin wannan lokacin da ta nutse cikin kogin tunanin shin ta mike ta dadaura wani abu ta shake kanta ta bar duniyar kowama ya huta ko ta mike ta dira ta tagar nan ta gudu idan safiya ta yi a nemeta a rasa? Ta jima tana kan wannan shawarwari biyu, wa'inda suka karrawaa kukanta karfi ta yadda tta ci kukan da bata taba irinsa a duniya ba, irin kukan nan da zaka iya fasaltashi da kana yi kana fatan dama mutuwa ka yi da irin wannan ranar? Irin kukan nan da shedan ke karra masa siga har ka ringa jijiga kana gannin ka zo duniya a banza ne, kukan kana yinsa ne kana auna rayuwarka tun daga lokacin da ka malaki hankalin kanka kana auna me ka yi da tsauri haka ta sameka,? Kuka ne kana yi kana tunanin aanya mutanen dake zagaye da kai sunna kaunarka kuwa? Irin kukan nan ne wasu kkan kashe kan nasu, wasu kuwa su fada a mugun hannun da zai basu shawarar guduwa............ Tun tana jin muryar kanta har ta dawo tamkar madiriritsi ya danneta tana ihu babu mai jinta A hankali yinwa ta fara dawo da ita a doron duniya Tun da sauran sawaye yinwar ta ringa kwakularta Karfin Adu'ar iyayenta ne? Allah ne ya yi ita din ba zata kashe kan nata ba? Ita dai yinwar nan ta sakata bude ido ta yi tsuru tana jin tashin hankali kamar ana rarakarta A hankali ta shiga auna yaya mutuwar kennan? Uwa uba idan ta je a wannan halin yaya zasu kare da walakiri kennan? Wai shinfidar kennan A hankali ta shiga tunanin iyaye A duka kaf abinda suka roka a wannan tashin na farko wanda shine na farko a tarihin rayuwarta cikin duban wanda suka yi mata Yau ko a shegiya suka haifeta sun mata adalci da basu bi da cikin ta magudadar ruwa ba Uwa uba suka jure shirme nata da sakalci A hankali ta gangaro kan wace bata yiwa laifi Idannuwanta ta rintse da zafin gaske da ta tuna kalaman innarta A hankali ta kawo maganar ɗa namijin kansa Haannayenta ta watsa tana tunanin wai a cikin wanda suke kira sarkinsu, da wanda take keta rantsuwar tana iya guduwa a kansa wane ya cencenci bijirewa iyayenta a kansa? Namiji dai sunnansa, zungundumin katon da ba miji yake a wajenta ba bale tace mijinta ne ai maganarsa na kan ta iyayenta Kennan yaya sunnantama? Zungureriyar yar iska marar rabo? Aminu baa ciwon yatsa yake yi ba, Aminu angwoncewa zai yi? Shi kuwa dayan azalumin za'a kai masa ni shima! A gaskiya a cikin biyu bata ga daya da zata bijirewa iyayenta saboda shi ba Manyan azalumen ya dace ta yi yaki da su, Ita marar gata ko? Iyayenta bayi? Abinda ya fi sakata tsanar rayuwar gidan tun tana yarinya idan mahaifiyarta ta tafi sai dare ya ratsa take dawowa, idan ba fitsari ta tashi yi tsakiyar dare ba bata ganninta, idan aka yi wasa sai a yi kwana biyu bata ga umanta ba! Mahaifinta kuwa yana fama bawon Allah, idan yana tare da ita kowani lokaci ana iya tashinsa dan aikin uban gidansa!, Ashe duka wannan bautar bata isa ta basu daraja ba? A banzan dai suke? Shine za'a tura yarsu yin kisa? Ita babu ruwanta da wani wai shi ANNEMOKAL ITIFAL!, abinda yake gabanta yaki da azaluman nan, dama ta rayu cikin farin ciki dan su zo tashi daya su wargaza? Lalle sun siya da kudinsu da suka saka Innar birni, Aban birni, da innarta kuka ris ris, ita kuma suka sakata summa! Maganar innarta ne, ba maganar soyaya bace, idan kuma taa gama aikin zai salameta! Wannan tunani ya kai hankalinta saman dardumar dake shinfide, a lokacin har asuba ta fara sanyo kai domin karfe hudun dare ta yi Jiki a sanyaye, kwonya cike da tunanin abinda yske kamar film ta shiga gabatar da sallalinta tana fatan wanda ya san inda ciwonta yake ya warkar mata, ........... Tabas BATA FARA DAN TA DAINA BA!, Aminu kuma yana nan daram a zuciyarta ba wai ya gogu ba, sai dai tana tunanin biyayar da zai yiwa innarsa itama zata kamaanta yiwa nata innar , sai dai shi ya fita cin riba, tunda shi aure zai raya, ita kuma CETON RAI za'a turata! Yanzu za'a fara 🤔☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️ *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣0️⃣ Kusan haka suka kwana, kowa na kaiwa Allah kukansa da neman sauki a wajensa Kamar yadda aka saba daukanta da duku duku hakan ce yauma, sai dai yau abinda ya sakata jin zuciyarta zata tarwatse Abanta kadai ne ke tsaye har aka karasa da ita dakin gyaran, bayan a da innarta na gefe, innar Birni na kai kawo abinta Kai ta gyadawa Abanta dake yi mata magana kasa kasa cewar ta yi kokari ta samu barci domin idannuwanta sun kumbura hulu hulu, hakama kumatunta Da ido ta raka shi, sannan ta gyara zamanta jiki a sanyaye tana jira ta ji an fara yi mata abinda aka saba Abanta na fita ya rasa ina zai nufa, shi kam tunda yake bai taba gannin yayar da kanwar sun yi fushi irin haka ba, Jiki ba karfi ya nufi ciki da niyar nufar dakin Inmar birni, sai ya tsinkayo maganarsu a kicin A hankali ya karasa ya dan labe yana sauraronsu, a tunaninsa har yanzu a cikin fushin suke tunda har ya ga babu wace ta damu da lekawa gannin an kai yarsa wajen gyara da sauransu "Aunty, aa, kar ki cire idon zakaran nan, sakashi walahi" Hindu ta fada da sauri tana tarewa ta saka shi a cikin dahuwar da suke yi FADIME ta dafe gaban goshi ta kai zaune tana fadin" Kin fi karfina Hindu, wannan dahuwar zaki ba yar taki? Walahi zaki sakata a uku bayan kin san komai" "Ni babu abinda na sani, hasalima babu abinda muka sani mu dukanmu aunty, ina kankanar mai yusufan? Gaskiya zuwa zan yi na kai mata tun jiya rabona da ita fa" Hindu ta fada tana turo baki FADIME ta yi yar dariya tana tafa hannu ta ce" Kin manta mun saka jaka goma goma, walahi idan kika je sai kin bani kudina, dan Allah ki barta mu gani ko ta yi hankali mana!, Haba kema, ke kin ce in na je wajen mijina kin ci jika goma, ni kuma in kika je wajen yarki na ci jaka goma, ehe" Yar dariya ce ta subuce masa har yana kama baki, kai kai kai, matan nan ba zasu taba girma ba idan sunna tare, watau haka aka dora dan a kuntata masa shi da y'arsa ko? Wani sukuni ya ji a cen kasan zuciyarsa, na ganewa da ya yi ba fushi mai sunna fushi suke yi da su ba, summa sunna ransu Juyawa ya yi ya nufi ciki zuciyarsa cike da dana sannin ihun da ya yiwa matarsa a kan abinda ta fi shi gaskiya,, ama in sha Allah zai bata hakuri, domin rayuwarsu da suka gina bisa aminci ne ba bisa fin karfi ba da zalunci irin na wasu mazan Abincin kari HINDU na mikawa masu mata gyara ta juyo ta komo suka ci gaba fa lamuransu ita da y'ar uwarta, hakan ya karra sakawa NADIRAH ciwon kai da zafin jiki mai zafin gaske, har ya zamto a yau gyaran safe kadai suka yi mata suka rakota da nufin ta koma ta huta , domin kana ganninta zaka gane bata yi barci ba , idannuwanta sun nuna Jiki a sanyaye ta idasa shiga falon da salama a bakinta, a lokacin HINDU na tsintar Zogalen da ta sa aka kawo mata danya sabuwa fill zata yi mata hadin tumaturi da kwai , shima gyara ne na musaman Muryarta bata fita da kyau ta sake yin salama sannan ta idasa shigowa jikinta ba karfi tana baza idannuwanta dan gannin Innarta ce kadai ko harda Innar birni? Gannin bata ga innar birni ba ya sakata sakin shagwabar da ta saka innarta zuba mata ido tana kallonta Raurau ta yi, nan da nan sai ga hawaye kamar an kunna pampo yana zuba ba kakautawa , sannan tana tsaye tana kallon Innarta, watau jira take yi sai ta fara zuwa inda take domin ai a ganninta itace ua dace su lalaba ba a ringa neman kasheta ba ko? Innarta ta kalli yayarta, ta kuma kallon NADIRAH Gefe ta matsar da zogalen tana mikewa ta ce" Wayo Allahna jaririyata, zo zo zo nan zo, wayo haka kawai saboda abin duniya na ki nemanki tun safe, zo, aunty zan biyaki kudinki bari mu yi waya da sarki!" Dariya ce ta kubucewa Fadime ta kirki, dan walahi har fruits din da tale yankawa ta ajiye tana rike ciki Dama ta san ba zata taba iya wuni bata nemo y'ar ba, ko a yanzu ta cikata da hirar Nadirar, uwa uba wai sarki, in Hindu ta takarkare tana labarin mijinta in bako ne kai sai ka duka ka gaisheta dan zaka yi tunanin sarkin garin gaba daya take nufi, koda yake, sarkin yake, sarki ne a rayuwarya, mutun tsayaye a kan lamarin iyalinsa, rashin karfinsa bai sakashi rayuwa a matse da iyalinsa ba, yana yin iya yinsa dan su rayu cikin farin ciki, ya daure mata kugu ita kuwa sai shagalinta take ita da y'arta Kuka NADIRAH ta barke da shi tana shigewa kirjin HINDU ta ce" Innata, fushi kike yi da ni? Innata shine ko ki leko ni?" A hankali ta dagotatana sake taba jikinta ta ce" Indi baki da lafiya ne? Kin ji jikinki kuwa?" NADIRAH ta mayar da kanta ta dora tana sake rintse idannuwanta ta ce " Innata, ki cema innar birni dan Allah ta yafe min kin ji? Ki ce mata ba zan bijire mata ba, ki ce mata ko me take so zan yi kin ji? Ta daina saurin yin kuka idan na bata mata kar aje na zama yar iska kin ji innata?" A hankali FADIME ta tsagaita dariyar da dama ba wai tun karfi bane ta daki murya take kyakyatawa tana kallonta A sanyaye ta dan kawar da kanta, daga garesu kirjinta na wani itin dokawa fat fat fat na tsagwaron kaunar gudan jinninta Bata shirya ba ta juyo da dubanta sanadiyar jin hannun NADIRAH a saman cinyarta ta rike a hankali ta ce" Innar Abana, ki yi hakuri kin ji? Ki yi hakuri innar Abana, tunda har Innata tace auren nan ba maganar soyaya bace, ceto ne, kuma idan komai ya wuce yana iya sawake min bayan ya gode min, Innata ba sai na zo na samu Aminun ba mu yi abinda ya dace?" FADIME ta zubawa fuskar Yarinyarta ido, a hankali ta ringa hangen tsagwaron yarinta a tare da yarinyar bayan ta daurari furucinta A hankali ta janyota jikinta ta rungumeta da runguma mai zafin nan, ya zamto kanta a saman kirjinta tana shafa bayanta kanshin turatenta gaba daya ya gogu a jikinsu kamar sunne suka shafa turaren, A hankali Innar birni ta ce" Allah ya yi miki albarka, Allah ya baki ikon cin galaba a kan makiya, in sha Allah daga yanzu da kika san komai zamu dawo ne munna gabatar da shirinmu bayan sun gams nasu, kafin nan mu tafi ki kwonta ki yi barci kin ji yar gidan innarta?" Wata irin ajiyar zuciya take karra saukewa tana jin wani dumi special daga kirjin mahaifiyarta marar cutarwa yana ratsa fuskarta, haka kuma murmushin mahaifiyar tata idan ta dago kai sai ta ji dama ya tsaya haka ta yi ta kallonsa kar ya katse Ajiyar zuciya, hadi da lalausan murmushi HINDU ta yi tana jin wani irin farin ciki na ratsa mata zuciyarta ta dubi FADIME dake dubanta niyarta ta kai NADIRAH ta kwontar da ita A hankali ta sakar mata murmushi tana girgiza kanta ta ce" Aunty ni da zan yi wancen, kaita dakinki dan Allah ta huta , na tabata bata yi barci ba, Indin innarta sai kin farka zan baki wani labari mai dadi kin ji?" NADIRAH ta gyada kai tana biye da mahaifiyarta nesa nesa kadan tana jin banbarakwai , domin bata saba haka ba sam Sunna shiga ta tsaya tana kallon maman nata dake gyara mata shinfidar Bayan mamanta ta gama ta juyo tana kallonta Wani murmushin ta sakar mata mai sanyi ta ce" Indi zo ki kwonta mana?, Cire wannan rufar ki kwonta ama banda safar , bara na gani cikin maganin Abanki ko akoy na zazabi na baki........" Motsin da ta ji a bayanta, kusa da bayi ya sakata juyowa da sauri Gannin mijinta ya sakata dan sada kai hadi da murza goshinta kamar wace kunya ta rufe din nan, sai kuma ta ce" Dama, dama innarta tace na shinfideta a wajena, kuma, kuma sai na ji kamar jikinta akoy zafi, shine nace bara na bata magani......" Murmushi ya saki yana kallonta, shi dama ya san harfa kunyar kar ta ja y'ar a jiki ace tana nunawa yar fari so yake sakata aikata wasu abubuwan Zagayawa ya yi yana sake dubanta ya ce" To ke da dakinki, magungunnan mijinki, da kuma yar hindunki sai kin fada min, kin ga ni na tafi masalaci a cen kuma zan yi la'asar da magariba, idan zan dawo ina son tuwo tukin Fadimatu Zahra" Kai ta karra sadawa, NADIRAH kuwa ta saki murmushi domin mahaifinta sai yar dariya yake yi mata sannan ya daga mata hannu ya fice A hankali ta karasa saman gadon ta hau tana sake bin mahaifiyarta da kallo, wace le boye nata murmushin itama , a ranta ta ayana' Irin rayuwarku na so samu, wace koda baku da yanci a tsakaninku akoy yanci, rayuwa mai cike da barkwonci da soyaya, bama tare da ku na lokaci mai tsayi ama na san a kan daya, daya sai ya bada kansa a sare, ina matukar girmamaku, ina kaunar dadadan amincinku, na so na gabatar da haka da Aminu, domin alamunsa sun nuna shima zai kasance uba, amini, masoyi, yaya a gareni, sai kuma ga bukatarku wace na rantse da wanda raina ke hannunsa koda hakan na nufin rasa numfashina zan aikata, domin ba haramun bane, ama na tabata in da rai da rabo, koda Aminu ya auri wata ni ya fara sanni a soyaya idan na dawo zai dubeni' Sai da ya narke mamanta ta zuba mata siga sannan ta karaso ta zauna a gefenta ta mika mata tana fadim" Shanye, da innarki ta sakaltaki magani sai an narkar an zuba siga" Murmushi ta yi mai sanyi, muryarta a sanyaye ta ce" Innar Abana, toh ki baki a bakina mana, innata ita ke bani na shanye kuma ta kama min kaina" Murmushi innar birni ta yi ta kama mata ta bata da kan nata, tana shanyewa ta bata ruwa, nanma ta sha sannan ta kama mata kanta ta yi mata ADU'A, kuma ta gyara mata kwonciyarta ta zauna a gefenta tana kallonta A hankali Nadirah ta dago idannuwanta tana kallon innar Birni, Innarta tace a duniya babu mai sonta irin innar birni, wannan magana ta tsaya.mata a zuciya har ta kori tsohon tunanin dake ranta A hankali ta ce" Innah?" Fadime ta kalli fuskarta NADIRAH ta ja numfashi kasa kasa ta ce" Innah, idan na tafi, shikenan ba zan kuma ganninku ba?" FADIME ta sake zuba mata ido, ta kasa ce mata A NADIRAH ta ce" Ta yiwu a ranar da aka kaini ya gane ba wace aka bashi bace ya saka a gilen kaina ko?" Kirjinta sai da ya doka, tana kallonta ta ce " Ki fadi alkhairi mana ko ki yi shiru INDI, sannan an ce bai san BAHIJA ba, ina gannin zuwanki ba damuwa bane tunda bai san wace tale y'ar sarkin ba" NADIRAH ta gyada kanta, kasa kasa ta ce" Innata, sai nake jin abin wani iri, yaya zan rayu a cikin mutanen da duke baki a wajena?, Yaya zan iya kaucewa kaidin masu kaidin cikinsu?, Yaya zan iya kare mutumen da ban wanene shi ba?" "Dama wanda ya isa ya kare ki daga dukkan abubuwan nan wanda ya baki aron numfashi ne NADIRAHNA, NADIRAH kowace mace bakuwa ake kaita bakon wajen da zata yi zaman aure, dama kuma rayuwa ta gaji ka zauna ka birge wani, wani ya tsaneka ba tare da ka aikata masa komai ba, halinka shine zai kwaceka NADIRAH................. sai maganar shi , shi Uban gidanki" FADIME ta fada tana shafa gefen fuskar NADIRAH a hankali NADIRAH ta dago lumsasun dara daran idannuwanta da mamaki ta ce" Uban gidana?" Mahaifiyarta ta gyada kai yana kallonta NADIRAH ta ce" Innata, kina nufin ni baiwarsa?" Mahaifiyarta ta zuba mata ido tana kallonta, NADIRAH ta mayar da kanta a hankali saman cinyar mahaifiyarta ta lumshe idannuwanta, muryarta cen ciki ta ce" Ni ba baiwa bace, sannan ni ba yar kaso bace.....Innatah, ba zan rayu a gaban kowa kamar yar kurkuku ba , ciki harfa UMUGHLUK ITIFAL!" A tsorace mahaifiyarta ta saka hannunta ta...... *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣1️⃣ A tsorace mahaifiyarta ta dago fuskarta tana kallonta ta ce" Me kike nufi?" NADIRAH ta tsare fuskar mahaifiyarta da kallo, tsoro, tarin shaka na bayana a saman fuskar mamanta, dan haka sai ta yi murmushi a hankali ta sake komawa tamkar mage ta lafe a jikin mamanta ta yi lamo bata ce komai ba, hakan ya sa mamanta mayar da hankali, ta ci gana da tsoratar da ita wanene UMUGHLUK ITIFAL, da jama'ar dake tare da shi, da tunatar da ita wacece ita, lalle baiwar take tunda yar bayi take Ita kuma a ranta murmushi kawai take yi, tana ayana abubuwa a ranta kamar haka' Ba zan je ko'ina na rayu kamar baiwa ba Innah, ban ce a aurani a kaini ba, ba kuma zan je a matsayin yar sarki ba, zan je a matsayina na ni NADIRAH, bayanshi bani da matsala da kowani sarki ko hadiminsa!, Ki kwontar da hankalinki, bauta ce ba zan yi ba innata' ................. Wannan shine mafarin shiryawar NADIRAH da iyayenta baki daya, sannan mabudi wata sabuwar rayuwa mai cike da sarkakiya da salo kala kala A wunin rana ana kula da jikinta ne da gyaran ciki kamar za'a cenzata baki daya Daga bakin lokacin da zata kasance da iyayenta su kuma nasu salon sunna kokarin karra taurara dukkan wani tsoron da zai sakata aikata aikin da za'a zo mata da shi dan a cutar da mutumen da suke kira Uban kowa ne....., Takan yi murmushi tace banda ita, ita kam ba ubanta bane gaskiya! Da zarar innar Abanta ta matsa kuwa wani rikitacen yare innarta ke yi mata mai tafe da rikitaciyar tafia mai wuyar fasara a kwakwaluwarta ita NADIRAHn innar kauye A gaban Innar birni sukan nuna mata Uban kowan nan uba ne ko kallonsa bai dace ta yi a cikin ido ba, innar birni na matsawa fakat Innar kauye ke fadin mace take, Allah ya gama bata komai tunda ya haliceta mace, a matsayinta na mace tana iya mayar da UBAN nan na Kowa dan jaririnta, ba aure ba, Allah ya sa mace dubu ya sani a duniya sannin ragage ne tunda mu'amalarsu ba ta shaƙar iskar junna bace, ta sunna ce!, Wai innar kauye ta dubeta duba irin na basira tace da ita zata fuskanci kamar bashi da lafiya, wannan rashin lafiyar tasa idan har ya yarda ya shiga harkarta zata yi wasa da ita, da rawa irin ta disko danser kugu a daure kafa a sama?, Ira innar Kauye ke cewa ta karkada kugu kamar zai tsinke fiye da dandali idan UBAN KOWAN cen ya shiga harkarta, to ira maganar gaba daya a duhu take zo mata kuma a dunkule, sai dai ta cira kaita kada kai ta fadawa kanta cewa ba zata dauki hudubar innarta ba, domin a hilacewar Innarta kamar tana son nuna mata zata je zaman aure, kamar yadda takan koya mata a da, bayan zam ne na ceto da rabuwa in sha Allah Tana cikin hayacinta da bin takun kowa a gidan nan, har yau da ya rage kwana uku a daura aurenta, sunna zaune tana jin yadda mararta ke mata wani irin nauyi aka zo da mota baka sidik da direba daya tak sai GIMBIYA, wace tana fitowa ta ga ikon Allah irin yadda mahaifiyarta da Innarta suka yi dan yi mata barka da sauka Kanta a sama, ko tace hancinta a sama ta yiwa NADIRAH kallo a hanzarce, sannan da ido ta yiwa Fadime alamun da ya saka Fadime saurin kama NADIRAH suka shige ciki watau uwar dakar FADIME Cike da isa ta idasa shigowa, fuska babu fara'a a tsaye tana kallon FADIME ta ce" Ina fatan, kin jadada mata wacece ita, haka kuma kin shaida mata me zai kaita BABAR FADA?" Fadime ta karra sada kanta ta ce" Na sanar Mata Allah ya taimakeki" Gimbiya ta karra duban NADIRAH sama da kasa tana mamakin kira, kyawun halitar yarinyar, sai ta ji a zuciyarta tana son yin kiran UMMA ta fada mata lalle lalle itama wannan a bata abinda aka ba matarsa ta farko ta sha, kar aje kilu ta janyo masu bam! Yarinyar ba abin wasa bace, bale a yanzu da take tsaye darrr Mahaifiyarta na duke? Ta saka mata wani shaka da tunani mai yawan gaske a ranta Kanta ta sake cirewa ta kuma duban FADIME ta ce " A nan zaku zauna har bayan auren, a yanzu na zo da BAHIJA, zata tare a nan, Fadime zaki kular min da yarinyata, dukkan abinda take so kamar yadda kika saba, ki sani da waya a gefena, kuma kasamcewarki a nan ba yana nufin kin tashi daga matsayin da kike bane kin fahimta?" NADIRAH ta sake saka idannuwanta tarr cikin na Gimbiya da ta sake juyowa ta kalleta, Gimbiyar ce ta cire idannuwanta tana kada kai ta dora da fadin" Kar na ji ko na ga labarin an barta ta fita, kuma kar ta yi bako ko bakuwa, domin jarida tuni ta fara yawo cewar za'a daura aurenta da ASADEEK!" a zabure FADIME ta dago ta kalli Gimbiya, sannan ta mayar da kanta kasa, subahanalah, Gimbiya ce ke kama sunnansa a waje gatsau hankali kwonce? Lalle ta shirya NADIRAH kuwa baki ta samu kanta da tabewa, a saman lebenta ta maimaita sunnan sannan ta watsra ta sake fuskantar matar nan da ta jima tana fata Allah ya nuna mata ta dauketa da mari a rayuwa "Sarki ya yanke cewa , ana gobe daurin aure zai zo ya dauketa da kansa ya wuce ta falonsa da ita dan gudun yan magana, ki karra jadadawa yarki biyaya itace makulin samun lafiyarku baki daya!" Ta sake fada a kausashe tana watsawa Nadirah wata mahaulaciyar harara, sai dai kikim din nan irin na yara masu taurin kai haka Nadirah ke tsaye bata sanyaya ba, a dole Gimbiya ta gama dukkan sharudan ta ta juya ta fita tana leleka dakunnan dan gannin wanda y'arta zata iya rayuwa a ciki! "Innah ki tashi mana ta fita " NADIRAH ta fada muryarta a raunane tana kallon mahaifiyarta Innarta ta dago tana murmushi ta ce" To indin Hindu bara na je na ga me zan mata?" Da sauro NADIRAH ta ce" Aa ki zauna bara na je na yi koma menene kin ji Innar Abana?" Kai ta girgiza tana ficewa, dan ta kula y'ar nan kamar bata jin nasihar a duka a gaban manyan nan sam, yaya NADIRAH zata tsaya kanta da kan Gimbiya? Kai subahanalah Sai da gimbiya ta samu rantsatsen daki aka saka kayan BAHIJA dake ta aikin waya sannan ta dubi Bahijar da sam bata damu ba ta ce" Daughter, kin dai ji abinda na fada maki ko? Ki yi kokari ku shirya da abanki, sannan ki yi iya yi ki ki rike kafarki da wayarki, ba kowa zaki yi hira da shi ba, ba kowa zai san inda kike ba" A dan kagauce tana magana da kawarta ta dan dakatar da ta ce" Momcy na fahimta gide, shima Papa din bai hadu da gayen bane, na masa uzuri da zarar sun hadu da kansa zai saka min albarka, momcy kin san Fadime ba zata iya aikina duka ba ko? Gaskiya ki san ta yadda zaki sama min baiwa ko dan murzawar jikina da susar baya, ita sam bata iya sosa baya ba gaskiya" Kai mahaifiyarta ta gyada tana kallon yar ta gama abinta ta shige dakin tana mayar da iPhone dinta kunnenta Ajiyar zuciya ta sauke tana ji zata yi missing din yarinyarta, sai dai ba komai zata jure in sha Allah ( uhum) Har bakin mota Fadime ta raka Gimbiya, har ta kama zata shiga ta juyo ta sake fuskantar FADIME a kausashe ta ce" Ina fata yarki bata fi karfin ki ba?" Fadime ta sake kallonta da mamaki Gimbiya ta dage kafadu ta ce" Dan bana son abinda zai je ya dawo, kar ki manta a hannuna ikon ci gaba da walwalarku take!, Na ga ta cika tsaurin ido ko rashin kunya ne? Kaina da nata a daidai da junna bata duka ba" Ajiyar zuciya Fadime ta yi, a sanyaye ta shiga bata hakuri , ita kuwa ta ja tsaki ta bude ta shige tana umartar Dorevmban kan su tafi Jiki ba karfi ta dawo dakin nata, dan sai take ji gaba daya gidan kuma a yanzu ya zama ba gidan da zasu wala ba, domin ita ta san wacece Bahija tun yarinyar na zannin goyo Tana bude dakin ta saka kafarta guda ta ji muryar yarta, kamar tana fada fada tana fadin" Kowani wawa sai ya taka mahaifana? Bayan biyayar da ta masu zata hakura da komai ta barwa Allah sai an biyota da shashashar magana? Idan Innar Abana ta yiwa wancen abar da ka kawo bauta Allah ya tsinen ......" "Cuta da malati dan ubanki makadi indi!" HINDU ta fada tana tareta hadi da buge mata baki NADIRAH ta janye tana kama abin gado ta ce" A lokacinda tace ASADEEK yake ko wa? Kiris ya rage na dauke yamutsatsen bakinta da mari!" "Lahaula wala kuwata ila bilah, NADIRAH, NADIRAH!" HINDU ta fada tana kaiwa zaune hadi da zarro ido Fadime da ta ji kamar zaninta zai kunce ya fadi dan tsorata ta tare a rikice ta maka kofar ta rufe ta karaso itama ta yi zaman yan borin a kusa da kanwarta Muryarta a raunane ta ce" Anya kuwa zata iya aikin nan? Innalilahi mun shiga uku,sunnan UMUGHLUK ne fa NADIRAH!" NADIRAHN ta tsare su da kallon mamaki, sunnansa? Haramun ne kamawa hala? Tsuru tsuru ta yi tana jin yadda mahaifiyarta ta cenza yare zuwa buzanci take fada makar zata ari baki, sannan ta nuna masu kofa ta kore su ita da Innarta, domin ba zata bari NADIRAH ta saka mata hawan jinni bs! Daga wannan ranar Nadirah ke gannin abin takaicin da ya fi kona mata zuciya Yarinya karama, ko wanka sai an cudata Sau biyu tana satar jiki da nufin zuwa ta cudata dan ta ci uwar babanta a bayin ana kamata a hannata zuwa! Yarinyar kan mike kafa innar birni ta murza mata Abubuwa dai da duka saka ta tsani sarauta!, Sai dai kashhhhh.....lamarin normal ne Fadime dai baiwa ce, Bahija kuwa yar sarki ce Yin hakan ba laifi bane, idan babu rashin mutunci da wulakanci, domin Bahija ke sanye da alkyaba, ita kuma da hijab irin na bayi. Kwonci tashi har ya zamto daurin aure za'a gabatar a gobe ranar asabar a sabuwar shekarar musulunci Cikin gari ya dauka, domin baki sun karaso an sauke su a manyan hotel da manyan gidajen masarautar Baki ne na gani na fada, baki ne masu daraja, domina ciki harda CHEIK wanda ke rike da sadaki, duda zuciyarsa cike take da zulumin rabuwarsa da UMUGHLUK ITIFAL, domin irin abinda UMUGHLUK ya nuna masa kamar auren nan da wata manufarsa ya amshe shi, uwa uba ya dauki Gimbiya da Auta sun tafi kauye wai, abinda bai taba yi ba, Umma kuwa itace ja gabar matan da zasu amshi yar sarki a matsayin matar UMUGHLUK ITIFAL su sadata da dakinta........................ Cikin masaurauta kuwa karya karyar da ake yi kai zaka yarda cewa eh lalle Bahija ake aurarwa idan ka gani, domin kai da fata baki da bayi sun mayar da hankali sunna gabatar da nasu kalar shirye shiryen aurar da yar tal , kwalin kwal yar gata yar sarki wa baban Sarki, wa zai bari a barshi a baya? A cen cikin falon mai martaba kuwa su uku ke tsaye, magana suke tamkar zasu kashe kansu, UMMA, SARKI, GIMBIYA Rai bace ya warci alkyabar da Gimbiya ke bashi wace za'a lulube NADIRAH da ita ya juya ya fice ta cen hanyar dake boyayiya a gidansa ya shiga motar da munafukin amintacensa ke jiransa suka dauki hanya............ A cikin falon kuwa UMMA ta maido dubanta kan GIMBIYA rai bace ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣2️⃣ Rai bace Umma ta ce da Gimbiya" Me yasa kuka cika yin sake da lamarin ASADEEK?, A kan me zaku yarda maganar nan ta fita daga bakunnanku? Dole sai kun sanar da wa'inda ke kasa da ku abinda yake faruwa?, Ashe karfin mulkin da kuke da shi a garin nan ba mai karfi bane da sai kun sanar da bayi da mutanen gari uwa uba mutanen dake karkashinku sunna cin shinkafa abinda yake faruwa?, Yanke hukunci naku ne, su kuma yin biyaya nasu ne, basu da zabi, basuda abin fada!, Ki san kin saka an yi yadda za'a yi da wa'inda suka san ainahin maganar nan, domin ba zan taba yarda maganar nan ta fita ba da sunna na a ciki!" Itama gimbiya cike da tashin hankali da kuma bacin rai ta ce" Ki daina yi min ihu a kai malama!" Da gautsi Umma ta ce" An maki ihu me zaki iya yi? Na ce me kike iya yi dan an maki ihu?" UMMA ta fan matsa dan har yawu Gimbiya ke patsa mata irin ranta ya yi mugun bacin nan Murmushi ta yi tana kare gaban fuskarta tana kallon Gimbiya, a tsanake ta ce" Ki tambayi mijinki girman darajata a zuciyar UBAN GIDANSA!, ki kiyayi hawa kan abinda baki sani ba, ba kowani bori ake yiwa dirar mikiya dan a sauke ba, wata jarabar ta fi karfin mutun sai dai Allah, Ki tsoraci baiwar da ta zamto Uwar sarki, ki sani kafin ta kai matakin sai da ta kawar abubuwan da ba zasu irgu ba......., Ta saka zuciyar sarki tafarfasa kuwa abu ne mai sauki GIMBIYA!" Daga nan ta koma wajen zamanta ta harde kafa tana jiran dawowar mai gidan Gimbiya haka take huci kamar zata fashe dan bacin rai, itama ta koma ta zauna tana sake cije lebe, wai wannan matar ce zata ce a kan me aka bar y'arta a cikin garin nan kuma aka barta da waya? Lalle itama bata san me take iya aikatawa a kan y'arta mace cilo ba! __________________________________ Da sauri ya karra shigowa ya kuma kallon matarsa dake tsaye a kofar bayi, a tausashe ya ce" Fisabililahi Innarta ace tunda asubahi nace ta zamto a shirye sai yanzu da mai martaba ke filin gidan nan ace min ta shiga bayi? Mai martaba ne ya zo daukanta ba aike ya yi ba fa" Itama yannayin fuskarta a dan rikice ta dube shi, ta sake komawa kusan bayin ta tsaya ta sake kwonkwasawa a hankali ta ce" Indin innarta, shin ba mun gama maganar nan bane da ke? Ki fito mana Indin innarta ko cikinki ne ya kunce?" NADIRAH dake tsaye ta sake hade bayanta da jikin kofar ta yi shiru, bata amsa su ba Mahaifiyarta ta fita da sauri ta janyo hannun HINDU dake kuka kamar zata mutu dan rabuwa da NADIRAH ta dungurota ta ce" Ba mun gama magana ba? Ban san me kuka tsara ba ki ce mata ta fito Sarki ke jiranta fa?" HINDU ta ja hanci ta cire kai ta ce" Ace, kamar yar da aka tsinto a jejin sambisa? Kowa na tsoron kar aje yar oga ce ta giga ta zama oga? Haba dan Allah ku ce masa a je da ni mana, fin karfin a ya yi yawa, banfa ce zan bita gidanta ba, ama a je da ni har a daura auren azaluman su tafi da ita mana ina tsaye ko?" Da takaici FADIME ta budi baki zata balbaleta da fada Abanta ya dakatar da ita ya ce" Ki je ki ce gatanan fitowa bara na bambare kofar tunda ba zata fito da laluma ba, ke kuwa Hindu Allah ya shirye ki" Kasa motsawa ta yi, ta je wajen sarki ita?, Har sai da Aban NADIRAH ya sake waigowa sannan ta fice da dan sauri ta fita Wajen motar ta nufa tana ta addu'a a cikin zuciyarta ta dan tsaya daga wajen direba zata buga sai gani ta yi an bude bayan da wannan kallon nasa na wuce gona da iri ya yi mata murmushi ya ce" Bata son rabuwa da ke ko Fadimata?" Da sauri ta ja baya sannan ta duka kasa gaba dayanta kanta a kasa ta furta" Barka da warhaka Allah ya karra maka lafiya" Ido yake kallonta da shi kamar zai cinyeta, sai kuma ya yi murmushi ya kada kai ya ce" Ban taba jin bana so a min kirari ba sai a kanki, tashi dan Allah ki sanar min bata son zuwa ne ko?" Fadime ta sake sadda kanta ta girgiza kanta da sauri ta ce" Allah ya karra maka lafiya wace ita zata ki bin umarninka? Allah ya hucii zuciyarka za'a fito da ita yanzu in sha Allah" Kai ya karra cirawa ya ce" Ta isa ta kiya, kuma ina mai tabbatar maki babu abinfa za'a yi, yarki ce fa Fadimata, yanzu sanar min, shin ta san abinda zata je yi kuwa? Kuma tabbatar min ta yarda da hakan kuwa? Jaddada min ai ba zata kiya ba ko?" Karra sada kanta ta yi gabanta na karra faduwa da irin girman zaluncin mutanen A sanyaye ta ce"Ba zata kiya ba, in sha Allah zata gabatar da komai bisa tsari" Murmushi ya yi yana gyada kansa ya sake duban hanyat, sannan ya karra kallonta ya ce" kin sani, abu ne da zai zamto farin ciki ma kowa, ciki harda ke da ita, domin yana kasancewa nine zan zamto mau mulkar AGADAZ, Fadimata hakan na nufin kema kin zama gimbiyar Agadaz, kuma ba zan taba bari wani abu ya sameta ba ai kin fahimta ko?, Ci gaban kowa ne da izinin Allah" Fadime ta lumshe idannuwanta, tana mayar da hawayen da ya taru a gurbinsu, bata ce komai ba, hakan ya daga hankalinsa, harma ya dan fitar da kafarsa ya ce" Ko akoy wata damuwa ne?" A hankali ta girgiza kanta ta ce" Dama, akoy kanwata, wace ta raini NADIRAr, Ita NADIRAH din ce ke kukan zata je da ita, ba cen bavan garin ba, iya Fada Allah ya taimakeka, da zarar an daura an tafi da ita, ita kuma sai ta dawo, shine tsaikon da aka samu, ama zasu fito yanzu in sha Allah " "Ita kanwar taki, bata da magana? Kuma ta san me ake nufi da maganar?" Ya fada yana sake kallon Innar birni Fadime ta gyada kanta ta ce" Ta san komai, sannan ta iya bakinta, hasalima tana tare da komai" Lebensa ya cije yana tuna irin rikicin da ya barro Umma tana ta masifar sun cika sake da abu da suka bari wasu suka san maganar bayan su biyu kadai, to idan ta ji ga wata ta karru yaya kennan? Baki ya tabe yana dage kafadu, domin a sanninsa shi ba sa'an yinta bane, sai dai ta nemi wasu daban Dan murmushi ya yi ya ce" To ai da kin fadi tun dazu da an jima da yi Fadimata, su zo mu je, kin ga dare na karra yi ,karfe tara za'a daura auren bana so hanya ta san da wucewarmu" Wata ajiyar zuciya ta sauke mai sanyi sannan ta mike ta juya da sauri, shi kuma har leke yake yi yana binta da kallo, sannan ya koma ya sake zaunawa a ransa yana ayana' To ko ke kika ce zaki je ai babu ubanda zai hanna Fadimata, ke dai rai da lafiya Gimbiyar Agadaz" Bata jima da shiga ba sai gasu sun fito A hankali ta tsaya daga dokin kofa tana hangensu har mahaifin NADIRAH ya gyara mata alkyabarta bayan ya sakata a motar, sannan Hindu ta shige gaba ta hakimce tana sake raya abinda ta yi niya, ai bataga ubanda zai hanna ba Walahi!, Fadime na tsaye har motar ta bacewa ganninta, a hankali ta dago idannuwanta ta sauke a fuskar mijinta, a hankali ta dora kanta a saman kirjinsa tana jan numfashi a hankali ta ce" Na hakura Abanta, Allah ya bata nasara" Kai ya gyada a hankali yana shafa bayanta shima a sanyaye ya ce" Allah zai rakata a dukkan motsinta, in sha Allah ba zasu sakata a uku ba" Da wannan suka shige ciki, a daren nan ma banda niyar kai goshinsu kasa babu abinda suka yi, haka kuma Fadima tana cike da zulumin lamarin Hindu, ita dai bata so ta aikata wani abin ___________________________________ Shigowarsu, bai saka daya daga cikin Umma ko Gimbiya motsawa ba, hasalima HINDU dake rike da ita suka fi tsarewa da ido su dukansu biyun Da waya a kunnensa ya shigo yana amsawa ya dube su da hannunsa ya masu alamun gatanan fa Gimbiya ta cire kanta gefe, Umma kuwa ta ciciba ta mike ta nufi inda suke tsaye sai yatsina take yi irin na raina bayin nan Tana zuwa HINDU ta koma gefe kanta a kasa, ita kuwa ta saka hannayenta cikin isa ta dauke Alkyabar da aka luluba a saman kan NADIRAH A hankali NADIRAH ta dago lumsasun kwartayen idannuwanta masu katon karfi a kan mai kallonsu sannan sun dauki kwali ga santsi da fuskarta ke nunawa koda babu maganar hoda ko makamanciyarta, lebenta kuwa banda walwal babu abinda yake yi na abin gyaran lebe da ake dan shafa mata,tamkar leben jarirai Gaban Umma sai da ya kwonci kwonci ya fadi, lokaci daya zuciyarta ta wani irin mahaukacin bugawa sannan ta saki alkyabar da sauri tana ja baya Jikinta har rawa rawa yake yi, da sauri ta juya ta damki hannun Sarki a gaban matarsa da kuma Hindu da ta zarro ido ta bisu da kallo ta ja shi cen ciki ta rufo kofa Hindu ta hadiye yawu a ranta ta ayana' Toh fa' Sunna shiga Umma ta dube shi kamar yadda yake kallonta ta ce" Cenza wace kuka ce zaku hada kuka yi? Wannan din wacece?" Murmushi ya yi ya kai zaune yana kallonta da kashe ido ya ce" Ke fa mayar mata ce,wannan dai ai kin san kamar guba take a wajenki ko?, Koda yake............lamarinki sai ke, ita dai ce yar bayin, yar Fadimata" Zaunawar ta yi itama tana mayar da numfashi ta ce " Lalle mace ce ita!, Ama ina fata ta yarda?" Kai ya gyada yana sake lumewarsa dan barcima zai wuce shi daga nan , dan da wuri zai farka saboda nadi da hawan da za'a yi kafin su wuce da amaryr Mikewa Umma ta yi tana sake daidaita numfashinta ta ce" bara na je na sauke su, ba za'a barta ta kwana a kasa ba, zata hau saman bed din ne" Kafadunsa ya dage, ita kuma ta fice Irin yadda ta ringa haba haba da su sai da abin ya basu mamaki gaba dayansu Shinfida mai kyau harda abinci mai kyau, sannan ta ringa jadadawa NADIRAH ta saki jikinta ita din ummansu ce, ita dai HINDU kiri kiri tana zaune dar tan kallonta , har sai da ta tsargu ta fice dan jin wacece wadda suke tare wai?, Tana fita Hindu ta zauna tana sake bin dakin da kallo NADIRAH ta kalleta ta ce"Innata matar nan warin munafukai take yi" Da sauri HINDU ta rufemata baku tana mata alamun ta yi shiru a kusa da su suke sannan ta sakar mata murmushi ta mata alamun ta zurra ido ________________________________ *Ranar dorawa budurwa daraja* Karfe tara aka yi za'a daura aure, sai dai abin bai kasantu ba sai kusan karfe goma na safe, a cikin masalacin da aka yiwa Sheik iso cewar a ciki za'a daira, bayan ga dumbin mutanne a waje da suka zo dan a daura da su Dayan abin da ya dan bashi mamaki gannin an ware mutanen da zasu kasance sheda basu fi a irga ba an ce sauran su zauna a waje dan AC baya yi, idan waje ya cinkushe hakan zai zamto takura ga mai martaba Shi dai ya gabatar da sadakinsu, sadaki mai daraja, sannan ya amshi auren da aka basu Sun daura aure cikin daraja da mutunci,sannan Sheik ya ja Adu'ar da har sai da Mai martaba ya fara tsitsine masa a ransa, gani yake wannan din ai iskanci ne, ina dalili wannan uban shishigi da janyi ayoyi haka? Daga nan SHEIK ya bude Alku'ani ya nemi da mutanen da suka zo tare su shigo, suka shiga gabatar da saukar alku'ani mai girma wanda hakan ya dake kular da sarki ya koma gefe yana sauraro ama hankalinsa ba a wajen ba, ya fi daukar hakan da wata fuska daban, su kuwa cikin nutsuwa suka yi, kuma kasancewar sunnada yawa nan da nan suka gama aka sake yin watga fatihar sannan aka shiga bayar da sadaka wa mabukata, wace wannanma kokarin Sheik din ne Bayan abubuwa sun lafa SHEIK na murmushi ya dake mikawa Mai martaba hannu a tausashe ya ce" Ashe sunnanta ba bahija bane?, Domin sai na ji kamar UMUGHLUK ITIFAL ya furta cewa sunnan yarinyar BAHIJA?" Wani irin murdawa da cikin Sarki ya yi sai da ya dan karkace zama,haka kuma idannuwansa sai da suka zarro lokaci daya ya shiga tunanin a ina UMUGHLUK ya san sunnan y'arsa? Lokaci daya kwakwaluwarsa ta tuno masa ai maganar ta farko su da kansu suka fada masa yarsu BAHIJA Wata boyayiyar ajiyar zuciya ya sauke ya ce" Ai Bahijar kiranye ne, asalin sunnan NADIRAH ne, Bahijar mahaifiyar ke so sai ta saka mata har kowa ke kiranta da hakan" Murmushi Sheikh ya yi yana daj sake kallon abin zufar da yake kokarin jike turkudin Sarki, sai kuma Sarkin ya mike yana fadin" Bara na je da kaina na ga shirin fitowarsu, sai na fito SHEIK" Fatan fitowa lafiya ya yi masa, sannan ya shiga buga numbar ASADEEK yana ayyana ' bawan Allah ko ka kira ka ji an daura lafiya? Gashi har karfe daya zata yi' A birkice ya shige bangarensa yana sake buga numbar UMMA, domin kwata kwata hankalinsa ya kasa kwonciya, so yake yi ya sake jin gaskiyar lamari cewa ASADEEK bai san y'arsa ba! Tana baza kanshi da sabuwar suturar da ta saka dan ta yagawa matan da suke takamar sunne darauta ta karaso ta rufe kofar tana sakin murmushin gannin ai kamar har hakarsu ta cinma ruwa tana fadin" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣3️⃣ Ba editing 😁 Tana murmushi ta ce" Barka da idasa aiki mafi hatsari Sarki, burinmu, farin cikinmu ya kusa tabata, baka ji yadda raina yake fari ba idan na tuna mun fara kaskantar da darajarsa kennan, duda mun dauko yarinya mai kyau zamu bashi, ama sai dai ya kalleta, domin na tashi daga shawarar cewa ba za'a bata abinda aka ba matarsa ta farko ba, dan kar aje ya yi ido hudu da ita ya nemi shafarta har ya kwatanta shigarta abu ya tabata mu bani!" "Asadeek ya san BAHIJA. Waje ne?" Ya fada yana tare numfashinta Ido ta zuba masa kafin ta ce" Wani abu aka yi ne?" A dan kufule ya ce" Ki bani amsa, ba ki maido min da tambaya da wata tambayar ba!" Kai ta girgiza tana fadin" Meye hadinsa da ita? A ina zai ganta? Mutumen da babu abinda ya shafe shi da harkar yan matan zamani bama, haka kuma yarka ta tsane shi ta yadda bata zuwa garin nan ta sauka a Fada, babu ta yadda za'ayi ya santa, menene dalilin tambayar nan?" Sarki ya ce" Wannan malamin nasa, wanda ke wakiltar aurensa ne yace min wai Ashe ba sunnanta bahija ba, wai Asadeek ne yace masa Bahija sunnan yarinyar?" Dan tsai ta yi, sai kuma ta yi murmushi tana fadin" Kai kam ka cika sarau, da bakinmu muka sanar masa sunnan nan, nima da bakina na sanar masa ya kai sau biyu, ina fata baka rikice ka tona kanka ba?" "Ni dai na ce masa Bahija kiranye ne da Mahaifiyarta ke yi mata, ama duda haka maganin nan da na baki bani shi nanna ajiyeshi a wajena, sai maganar aurensa ta lafa sosai za'a fitar da shi a kai mata, kar a bata shi yau" ya fada yana miko mata hannu Itama murmushi ta yi, domin a gaskiya idan aka ce daga zuwan yarinyar har ta aikata aikin nan an kamata itama ba zata ji dadi ba, haka kawai take jin bata taba gannin macen da ta dauki hankalinta irin yarinyar nan ba, ciki harda wancen uwar taurin kan da ta zabi hauka a kan hankali, Maganin ta lalubo a cikin rigarta ta miko masa, tasakashi a ledoji ta masa wani irin dauri,shi kuma ya juya ya kai shi ya boye sannan ya dawo ya tsaya still idannuwansa ba daidai ba ya ce" Idan kuka bata magani me kennan?, Ai zan so ya gwada tashin jarabarsa a kanta,ya ki zuwa inda take da tsoron kar ya je abu ya kwonta, da wannan damar nake so ki saka masa ido, ta yadda zaki turamasa baiwa tsirara, ko waye shi zamu gani ai, idan ya aikata abinda a kansa yake jefe mutun har lahira sai mu gani, jefe shi za'a yi ko gubar macijin nan zai ci?, Ki barni in sha dadin kallonsa a mazinaci mana kema" Ido ta kankance tana kallonsa kafin ta ce" Bam taba gannin mugu irinka ba, ama wannan tunani ya min , lalle lalle idan haka ya tabata ni nan nice zan tunasar da shi shine fa mai yankewa wani hukunci, yaya kennan?, Uhum ka hango shi a cikin rami kansa a waje, idan na tashi daukan dutsin da zan jefa masa sai na dauko rungumeme na zafta masa ta yadda zai makance kafin ya mutu!" Wani irin murmushi ya yi yana hangen komai a idannuwansa, a matsayinsa na wanda ya haura shekaru sittin a duniya, yana hango wasu sittin din ne a gabansa? Fa karfinsa? Da hankalinsa? Wai idanma mutuwa bata ratso a lamarin ba, gigita irin na tsufa fa? Wanda ke saka bawa ya dawo tamkar jariri fa? Tsufan da ya zo maka da tsoron Allah da zikirima yaya kake dawowa idan shekarun sunna dauko da yawa? Bale tsufa irin nasa? Allah, kar ka hadamu da makantar zuciya Ya Allah, Allah idan har munada rabon yin makanta cikin biyu gwara mu rasa ganninmu da zuciyarmu ta rufe, domin idan muka rasa ganni irin na hasken musulunci idannuwan namu zasu hasko mana gigitacen ganni a duniya da kiyama! Agogo ya duba sannan ya kalleta ya ce" Ki je ku fara shiryawa, ki kula da WA'INDA zasu shiga motocinku, da zararan fito daga sallah zaku dauki hanya saboda ku samu shiga da duhu duhu dan kiyaye dokar shiga da Matar sarki da hasken gari" Kai ta gyada da murmushi ta fito ta sake ratsawa ta nufo bangaren GIMBIYA Tana zuwa ko Gimbiyar bata kula ba ta nufi dakin BAHIJA wanda aka sauki su NADIRAH da HINDU Tana kama kofar zata shiga ta ringa jiyo kuskuskus, irin magana ake yi kasa kasa sosai A hankali ta dan labe sannan ta karra kunnenta, dan gaba daya ita bata wani yarda da marakiyar yarinyar nan ba, "Kina jina Indin Innarta, ki sani su din sun isa da ke, sarakunan ki ne, da mu baki daya, su muka sani, kuma dole mu masu biyaya kin ji? Ki tabatar kin masu abinda suke so fa?, Idan yau akace ki aikata ki aikata shi, mu mun yarda da su, kuma ko me suka sakamu zamu aikata masu ne dan kauna" NADIRAH da ta ci kukan jin ana fadar cewa an daura aure an daura aure ta sada kanta , domin bakinta ba zai iya furta komai ba, haka kuma rarashin da Innarta ke yi mata ta jiyar da maganar gannin innuwar mutun ba zata iya amsa ba a yanzu, batada karfin amsa maganar nan gaba daya, shin yaya zata yi da ranta ne? Yau an wayi gari an daura mata aure da wanda batama sanshi ba, shima bai santa ba, bata taba ganninsa ba, Aminunta yana LABA baima sani ba, daga ce masa zata rako innarta biki su dawo, an dora mata alkyaba, an nadeta, an dora mata igiyar da ta fi kowace daraja da nauyi a wuyana, wai a yanzu ita matar wani ce, waninma sarki, ta yiwu tsoho ne takwaf bawan Allah tunda ta ji su ummanta na kiransa baban kowa?, Ta yiwu shiruftar tsufa ta kama shi, ta yiwu kuma wani kasurgumin azalumin boye ne, mutumen da ya saka a kasshe baya ce masa komai? Shikenan an daura aurenta innarta bata saka dinkin da tace zata yi ba, sannan ba'a siya mata gadon karfe mai rumfa ba, shikenan za'a kaita wajen da bata san me zata tarda a cen ba, shikenan za'a yi bikinta babu mahaifanta a gefenta,ko innar birni tana tunata? Ko ta manta da ita? Abanta ko ya dangana ? Ko yana cike da tunaninta?, Haba ta yayama zata iya bada amsar wani wasan kwaikwayo na innarta? Bakinta ba zai iya ba sam! "Ki daina hawayen mana na ce kin ji yar gidan Indinta?" hHindu ta sake fada tana sake satar kallon kofar Shigowa Umma ta yi ta mayar da kofar ta rufe ruf ta karaso ciki sosai tana kallonsu daya bayan daya A nutse ta ce" Kukan me take yi ita kuma?" HINDU ta ja ajiyar zuciya, irin abin a ranta ta dubeta sannan ta sada kai ta ce" Allah ya karra maki lafiya, dama ita din da saurayinta wanda take so sosai, to da aka daura ne take dan kuka da cin alwashin ta fiku zakuwa ta aikata aikin nan dan ta dawowa saurayinta" Cike da tsare gida Umma ta ce" Aikin me zata aikata mana?" HINDU ta dago tana kallonta, irin zata mayse mata lambar nan? Ko ta cire kanta a ciki?, Bata san barikima iyawa bace kennan? Hindu ta sada kanta, irin ta dan daburce, sai kuma ta dago cike da confidence, watau ta matukar yarda da ita a wannan fannin ta ce" Ina magana ne a kan, aure aka daura mata, dole ta je ta yi biyaya, idan ta dawoma zata tardo saurayinta, ama bawa yake a gareta, domin talaka ne!" Umma ta sake kurre Hindu da kallon mamaki, lalle wannan din wata biyayiyar muguwa ce, ta ayana a zuciyarta, watau ta ji maganarsu ta bayan kofa, ta zata tare suke ta karra bata magana a jumulce, ta nemi karin haske ta kuma zagayeta Zaunawa ta yi tana fadin" Wacece ke?, Ina nufin menene tsakaninki da ita?" HINDU ta dubi NADIRAH, ta dubi UMMA, a hankali ta ce" Ni na raineta" "Wani irin raino kika bata?" H umma ta tambaya HINDU ta lumshe idannuwanta ta ce" Na horeta ne cewa, biyan bukata rai ba a bakin komai yake ba, ta fi yarda da fansa a kan komai, hakan ya sa ta kasance amintaciyar baiwa!" Wani irin yarda da Hindu ke darsuwa a zuciyar Umma, sai dai sam bata nuna ba, hasalima mikewa ta yi ta karasa wajen akwatin da suka zo da ita ta zauna ta bude ta shiga ciro suturar da ita da kanta sai da ta yi mamaki, domin sakon daga matar UMUGHLUK ITIBEL ne cewa sakon amarya ne kyauta ce daga ita, ita kuma ta dauko bata duba ba dan ta san ba zai wuce kayan da za'a sakawa amarya ba, ta tabata kuma ba zata yi wani abin kirki ba dan bata iya abu irin na fita kunya ba, sai dai a yanzu ta yi dana sannin rashin budewar, da ta rage wasu abubuwan, koma ta cenza su Sarkar ta zinari ta sake zubawa ido, sai kuma ta tabe baki, ko menene zata dauke daga baya ai Kayan ta miko ma HINDU tana kallonta a hankali ta ce" Ki shiryata" Hindu ta amsa ta mike ta ce" Tashi mu shiga ciki" Umma ta dan dago ta sake raka su da kallo har suka shige Murmushi ta yi tana karra jin yarinyar na wani irin karra mamaye mata kirji, ita abin har ya farra damunta, anya kuwa zata aikata abinda Gimbiya ke so? Watau idan yarinyar ta kashe sarki a yi yadda za'a gane itace ta kashe shi? Anya zata iya aikata haka? Yarinyar wata irin salihar fuska mai dukkan kirji ne da ita Sun dan dauki lokaci sannan suka fito A yanzuma kasa dauke idannuwanta ta yi a kan NADIRAH har HINDU ta zaunar da Madirar a gefe sannan ta sake gyara mata daurin dan kwalinta ta kuma kallon Umma tana jin lalle idan akoy wace ya dace su yi shayi wannan matar ce, dan kuwa gaskiyar NADIRAH tana tare da abin munafurci a tare da ita Umma ta dauke kanta ta ce" Kina da aure ne?" HINDU ta sake kallonta a hankali ta ce" To dada, gani nan dai, auren dai gayanan dai, kawai" "Kina da aure ne?" Umma ta maimaita a dake, domin amsar bata yi mata ba Hindu ta gyada kai ta ce" Eh " UMMA ta kawar da kanta ta mike ta dauko alkyabar da za'a lulubawa MADIRAH da safa da kuma baban abin rufa na turkudi mai masifar tsada da za'a lafta mata ta mikowa HINDU sannan ta kama hanyar fita tana fadin " Ki iya bakinki, masoyansa a garin da ba nasa bama sun fi makiyansa yawa, ku kasance cikin shiri koda yaushe muna iya kama hanya" Tana fita ta daga wayar wa'inda ke tsare da hanyar saboda REBEL ( watau yan fashi da makami) ta tabatar an watsa mutane ta ko'ina da bindigogi dauke da alburusai, domin gari ya dauka ya yi aure, idan akoy masoyansa a daji, akoy makiyansa masu farautar rayuwarsa a bayane! Ke kuma aboue ko? *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣4️⃣ Tana tafia NADIRAH ta dago, muryarta a cen ciki ta ce" Innata, idan kika bi ni Aban kauye fa?" HINDU ta lumsje idannuwanta sannan ta yi murmushi, a sanyaye ta ce" Ba zasu kwace mana komai ba Indina, zan raka ki har dakinki sannan na dawo in sha Allah, ki min alfarma ki kwontar da hankalinki kin ji?" Kai ta gyada tana jin sanyi sanyi a ranta, sannan ta karra jimke yar karamar wayar da Abanta ya bata cewar akoy layinsu a ciki, yanzu haka Innarta ta daukota daga ma'adanarta ne dan su yi magana da iyayen nata, sun gama maganarma ama ta kasa mayarwa, da kyar ta ba Innarta ta mayar ta boye sannan suka mike dan gabatar da sallah Bayan an gama sallar azahar aka shiga fitar da kayan da aka ce nata nw, kayan da su ba'ama nuna masu ba Lalle an fitar da kaya masu yawan gaske sannan aka fitar da ita Gimbiya ke rike da ita, irin rikon nan na tana jikinta sosai sannan tana ta shafa kanta tana afkin nuni da rarashi take yi har suka karaso gaban wuleliyar motar da za'a sakata suka shigar da ita sannan suka yi salama aka dauki hanya, domin tafia ce zasu yi a hankali wace zasu dauki lokaci koda sun shiga garin da wuri ba zasu isa gidan da wuri ba sai sawaye sun dauke, dan ba'a zuwa da matar sarki ido na gani A hankali suke tafe, cikin motocinsu, motocin sojawa sun zagaye su, tafiya wace idan sun doso ake dakatar da masu zuwa sai sun wuce har suka dauki babar hanyar da zata kai su AGADAZ A hankali Umma ta dan karkata kusa da kunnen NADIRAH ta ce" Kuka kike yi?" NADIRAH ta dan yi tsam, kafin ta girgiza kanta a hankali" UMMA ta yi murmushi ta ce" Kina iya kwontawa a cinyana, ko a kafada ki huta kafin mu isa BABAN birni, domin zan so ki bude ido ki ga Baban birni, ko kin taba shigowa?" NADIRAH ta sake girgiza kanta tana dan gyara zamanta Umma ta sake yin murmushi ta ce" Garin Agadaz, gari ne dake dauke da al'adu, da kuma yannayin ginni irin na kasa, Mazan garin sunna da kudi , boyayun kudi, mahaukatan kudi, domin wasunsu manya ne na kasa, wasu kuma manyan da suka aikata fashi da makami a da ne, wasun ma'aikatan gwamnati ne, wasu masu cin gashin kansu ne, muna cakule da larabawa, da kuma wasu daidaikun yaren........, Gari ne mai daraja, mai girma, mai dauke da mata buzaye da larabawa masu ji da kansu harma da daidaikun wasu yaren, a Agadaz muna girmama Uban kowa, Shi UMUGHLUK ITIBEL yana zuciyoyin samari da yan mata, datawa da tsofafi.............., Zan iya ce maki kin yi dace kin kuma taka sa'ar da duban yan mata ke hari....kin kafa tarihi koda a yanzu kika mutu" NADIRAH ta dan dago da idannuwanta ta dan saci kallon Umma, still bata furta mata koda A ba Umma ta dora da fadin" Abinda ya sa ba'a cika gini irin na bulo da bulo ba sai gidan wa'inda suka gagara, saboda sahara, yankin kasa da kuma tsohon gurbi na Volcan, idan zaka dora ginnin da ba kasa ba ko zana, tabas sai ka girgiza da aljihunka, sai dai idan ka tara hakan ba wani matsala bane kuma sai ka zuba cefa ka zuba ginni, Mijinki ya yi ginnin da harta dakin shn shayinsa Bulo ne.............., Ya tara fa, ke kam kin yi dace" NADIRAH ta tabe bakinta a ranta tana ayanna' hakane' Umma ta ce" Zaki sha mamakin darajar da zaki samu, duda ba ainahin ke din bace, ama ke dinma kece, tun daga wajen gari matasa na cen da manyan motoci sun yi niya sai sun yi wasan dauko Amarya duda shi angon ba kece a gabansa ba, ya fita da mahaulaciyar kanwarsa da kuma matarsa shakatawa......, Wannanma ai kamar cin amana ne ko?" Wani murmushi ne ya kwacewa NADIRAH, a ranta ta ayana' An zo wajen, dama na fadawa Innata kina warin munafukai, da ace ita din ce ta yiwu hakan ya mata ciwo, sai dai kashhhhh ko a kwalar rigata' Umma ta karra rage muryarta ta ce" kin san manyan ginni na matan gidan hudu ne, daya matarsa na ciki, daya sai ya saka kanwarsa, kema a dayan kike na kusa da na kanwar tasa, na san dayan kuwa rushe shi zai yi dan da wahala wata macen ta shigo a matsayin matarsa ko?" Lalle A yau a yanzu NADIRAH sai ta rainawa matar nan wayo, kuma ta tabata wannan mata tana fama da jahilci mai tsananin gaske, wanda ba zai iya barinta tunanin fari ko baki ba, sai dai ta aikata abu kanta sake, tabas tana da ayar tambaya a kan matar nan, magangannunta sunna saba kamaninta, sai dai ba zata yi gagawa ba, dan bata san wacece ita a masarautar da wajen baban nasu ba sam, Sun ja tafiyar iya ja, har sai da duhun magariga ya fara shigowa sannan suka saki tafiyar suka yi mai sauri suka karasa ana gama sallah A hankali NADIRAH ta samu kanta da dan ba idannuwanta damar kallon hayaniyar da take ji A hankali ta fara kallon yadda innarta ke washe baki tana daga hannu Wani murmushi ne ya kwace mata dan tsakanin Innarta da Allah take daga hannayenta bibiyu tana gaishe da masu gaisheta Da sauri ta damu kanta da karra wara ido tana kallon tarin jere na motoci da dawakai majiya karfi, da manyan babura sun tsara abin gefe da gefe sunna gabatar da wasan a tsare Karra zubawa abin ido ta yi tana jin wani irin yamyamyam a jikinta, domin wasa ne na kwararun wa'inda suka iya sarafa mota, ko babur, uwa uba DAWAKAn da suka sha ado , ga wata mahaukaciyar busa da manyan makadan kwararu masu gadon abin a jinninsu sunna aiko da busa da kida irin na sarauta sunna karra rike gangar kamar zasu tada wajen Tabas abin ya kayatar da ita, a hankali kunnenta ya tsinkayo mata muryar Umma tna fadin" Murna suke yi, farin ciki suke yi, burinsu suke gannin har ya cika, Uban gidansu mai tausayin talakawa ya karra aure, ta yiwu a yanzu su samu magaji mai halin datako, sunna farin ciki ne dan burinsu a wayi gari matar UMUGHLUK ITIBEL ta dauki ciki, uwa uba ta haife masu , a yanzu kyauta zaki gabatar masu ta wani abun dake jikinki, ko menene, kina iya basu zoben nan, ba kudinsa zasu auna ba, darajarsa da ya fito daga wajenki zasu duba, idan mun karasa Fada an fito da ke zaki yi kyautar" Janye idannuwanta ta yi daga kanta, yanzuma bata ce mata komai ba, hakan ya sa Umma karra kallonta, ikon Allah take ta kallo, bata taba gannin yar bayi da saurin daukan abin sarauta a jinni ba irin na yarinyar nan! Get din gaba daya aka wangale motar dake dauke da ita kadai ta hau baban hanyar su kuwa du suka layu ana ta buda irin ta bugaje ana yi mata oyoyo Umma ta fara fitowa bayan ta sanar da Innar Kauye cewa ta dakata har a mikata dakinta sai ta shiga, idan ta shiga kar ta zauna a saman kujera ta zauna a kasa har a gama gaishe su a watse Ita dai NADIRAH tana zaune ta ji Umma ta kamota, a kasan zuciyarta ta rinha addu'ar da Innar birni ta koya mata cewa ta shiga da ita du inda za'a sakata A hankali ta dan dakata da Adu'ar ta zubawa hannunta dake cikin na umma ido sakamakon jin da ta yi tana dan murza mata hannu A hankali ta janye hannunta tana mayar da shi kirjinta sannan ta ringa bin sawun Ummar wace ke ta son karra lalubo hannunta A kofar tamfatsetsen falonta Aka ja aka tsaya da ita Da wata irin isa da kuma iy sarafa harshe Umma ke yi masu godiya, ta gabatar da NADIRAH a matsayin yar sarkin Tanut sannan mata a wajen Sarkinsu Sosai wajen ya karra daukan budar farin ciki A hankali ta juyo wajen NADIRAH kasa kasa ta ce" Ki kwatanta kyautarki wa jarumin matasan garin nan baki daya dan ya isar da sakon wa matasa" Dan tsai ts sake yi, a hankali ta sake yin yadda zata hangi taron mutanen nan, har jikinta wani irin rawa yake yi idan ta ga wai taronta ne, a gaskiya ta haka ta yarda ko yayane yanada masoya shi baban nasu, domin ba'a yiwa talaka dole, koda an sayi wasu a cikin talakawa wasu ba zasu sayu ba, wandinnan jama'ar kuwa da du fadin masarautar nan ta ki daukansu ta tabata sa kai ne, yan gani a kasheni ne a kan sarkinsu A hankali ta kai hannunta wuyanta ta bale tafkekiyar sarkar nan ta zinari, ta cire awarwarayen zinarin gaba daya tana murmushi ta fitar da farin hannunta wanda shi an ganshi sanadiyar hasken wajen na fitilu ta mikowa UMMA wace ta yi mutuwar tsaye ta kasa karba har sai da ta budi baki kasa kasa sosai ta ce" Kadan ne, Allah ya sa zasu ji dadin karamawata, na gode" Wani irkn abu ya sara a gefen kan UMMA, maganarta jakadiyar UMUGHLUK ITIBEL ta ji, nan take ta daga murya ta rangada buda tana sheda kalaman uwar gijiyarta, A dole Umma ta amshi sakon, tana ji tana gani ta mikawa Hakadiyar sarki sannan ta juya ta budewa NADIRAH kofa tana kallonta har ta gama murmushin tana jin kamar ta cire alkyabar nan ta kwaso shokiiii ta juyo ta shiga falon da take kyautata zaton na sarkin ne ko? Domin tana shiga ta tiles din dake malale ta fara tunanin nan din dakin mai gidan ne gaba daya Rufewar kofar da muryar Umma kamar cikin fada fada tana fadin" A kan wani dalili zaki dauki zinari irin wannan ki ba wa'inda basu san darajarta ba, ba zasu iya bata darajar da take da ita ba, ko dan kema ba sannin darajar tata kika yi bane?" Da mamaki ta dan zubawa Umma ido, a hankali ta dake zuba mata wani kallon da ya daka Umma dan sasauta muryarya dan sai take gannin kamar yarinyar na yi mata kakausan kallo ne, gashi bata riga ta san har ina yarinyar ta kai da iya juya nata mumunan halin ba, ba zata so a yanzu wannan ta zame mata matsala ba sam Dan murmushi NADIRAH ta yi ta ce" Na ji kin ce a karamasu, kuma na ga ku manyan sarakai ne ko?" Umma ta karra zuba mata ido tana nazartarta Hakan ya saka NADIRAH dan waskewa tana dafe goshinta ta ce" Baki ji zuciyata ba, Wai dan Allah zinari ne ko menene? Ki ce min karfe ne marar tsada , walahi idan zinari ne zan iya neman wanda zai je ya sato min abina a daren yau!" Da takaici Umma na sauke boyayiyar ajiyar zuciya na damun nutsuwar tunaninta ta lai zaune ta ce" Ba maganar ki tura a sato maki, ke da muke so ko menene ki zamto a boye ba a bayane ba? , Kawai kin yi n farko gaba sai ki kiyaye, ki cire alkyabar mana ki huta? Sai fama kike gashi da an ganni ana gane tana wahalar da ke" NADIRAH ta dan yi murmushi tana girgiza kanta ta zauna itama a saman kujera bata ce komai ba, a ranta tana ta karra yin waje tana ajiye Umma Mikewa Umma ta yi tana fadin" Ohk, ni zan je bangarena na huta, na gaji sosai, sai da safe" NADIRAH ta yi mata murmushin da ya sakata sake kureta da ido, sannan ta fita a ranta tana ayana a yau dolema ta samu yarinyar da zata dan abinnan, dan gaba daya jikinta har rawa yake idan tana kallon yarinyar cen.....lalle sai ta mayar da son banzanta gefe ta sakarwa yarinyar cen kudi ta yadda zata yi gagawar siyanta, dan ta kula itama mai son banza ce! Nadirah, kallon Innarta kawia take yi, sai karra bayani take du ta rude na girman gidan nan sannan ta sauke ajiyar zuciya tana kallonta ta ce" Indi, gaba daya na fara tsorata, anya zamu iya kuwa?" NADIRAH ta sauke ajiyar zuciya ta yaye alkyabar nan hadi da mikewa tana jan zip din watsetsiyar shadar da aka watsa mata a hankali ta ce" Allah zai doramu a kansu in sha Allah" ___________________________________ "Yaushe zamu koma ne Sarkina?,, Kanwata ta tare ba nan, ya dace ace ni na amsheta na tarbeta fa"............... Matarsa ke fada a hankali bayan ta zauna a kusa da shi sosai tana kallonsa Idannuwansa, masu kashe mata jiki da sakata a yannayi na bege ya zuba mata, sai kuma ya yi dan murmushi ya dauke idannuwan nasa yana tunanin wunin da suka yi yau da Auta, irin hirar da suka sha hankali kwonce, har waya ta yi da mijinta normal, daga baya na da tace masa yaushe zai zo su tafi sula yi fada dan yace yana jira a bashi dama, sarki yace zai tabo shi, sai ta samu lafiya, daga nan ne suka yi fada Shi abinda yake mashi mamaki da ciwon auta kamar bata son zama a fada, ko tunanin iyayensu ke hadasa mata rikicewar yannayi ne? A hankali ya kai idannuwansa saman hannun Matarsa, wace ta sakalo da hannun wajen cikinsa a hankali ta shafa cikin nasa, sannan ta kawo kanta wajen wuyansa ta ajiye tana sauke masa numfashi kasa kasa ta ce" Baka ra'ayin, ko shafaka ne na yi, ka samu nutsuwa?, Ta haka kana iya zuba min nutsuwar taka fa, sai ka ga na samu ciki................" Idannuwansa ya lumshe, kirjinsa ya fara daukan zafi zafi hadi da caji, A hankali ya dan karra riketa, sai dai yanzu ta masa wani rikon da ya fi na dazu watau gaba dayanta tana neman kanainaye shi ne Idannuwansa da suka fara zama wasu kala ya bude ya sauke a saman fuskarta, a hankali yake kallon lebenta da lalausar fatarta Bugawar kirjinsa na karra hauhawa, yannayinsa na neman fin karfinsa ya sake riketa kam a jikinsa bale da ya ji hannunta ya kai babar jihar da take rufe tana hutawa, wace ke fushi take iya amayar da fushinta a kowani lokaci Da sauro ya kai hannunsa ya............. 🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢🫢 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣5️⃣ Da sauri ya kai hannunsa yana kallonta, idannuwansa da suke karra juyewa ya sake dora mata , muryarsa cen ciki ya ce" Bana tunanin, wasa da ni zai rage wani abin, sai dai ya tado abinda ke Kwonce girl" Harshenta ta ciro a hankali ta shiga lasar wuyansa, haka kuma hannun nasa ta sake rike abinda yake nufin ksr ta rike din Gaba daya , lokaci daya, ya nemi ficewa a hayacinsa Idannuwansa ya karra rintsewa, jikinsa ya ringa amsa, domin abu kankani ke iya tayar da shi, ko dan a jike yake?.....da wani karfi kadan ya sake damje haannayenta a hankali ya furta" Kar ki rikitamu, bayan kin san ba zamu anfani junna ba...." Idannuwanta dake zubar da hawaye ta dago tana mai zumudin son gannin abin nan a bayane yau ta zuba masa idannuwanta muryarta a raunane ta ce" Kana iya samun nutsuwa fa ba tare da ka shigeni ba, ka bari na yi abinda na karanta a labaru da kwatance, ka bari na kwatanta ko yau zaka zubar da ciwon nan" Kansa ya girgiza a hankali yana saka hannunsa ya riketa wannan karron rikon da ya hannata wani motsi yana kallonta, sam bakinsa ya gaza furta mata wani abin, sai abin wuyansa dake ta sama yana kasa, fuskarsa ta dauki wani irin ja, lebensa ya yi kamar ya dan kumbura, haka kuma idannuwansa jansu har ya so ya zarce misali A hankali ta kifa kanta a saman abin kujerar tana hadiye kukanta, ita abinda ya fi damunta irin ya bari su ringa wasan da za yana taimaka masu wajen rage masu sha'awama baya yarda, kwata kwata baya yarda, abin ya masa yawa jama'a, ita fa da sauki, walahi da sauki ita, shi ya fi bada tausayi, baby gaba babu baya, matsalar ta masa yawa jama'a, kuma ya bari irin abinda take koya a karance karance ta ringa yi masa sai ya kiya, sai yace shi ya san kansa, ba zai taba bari ya aikata haka ba, domin cutar zata koma ta kwonta a cikinsa, a yadda ya giga ya fi karfin a matsashi ya rabu da malati, ya fi karfin haka A hankali ta dago fuskarta, muryarta a raunane ta ce" Ka san menene UMUGHLUK?, Ta yiwu idan ka gwada da wata macen fa ka kai ga ci" Idannuwansa a lumshe suke, a haka ya dauki minti kusan hudu da yin maganarta bau bude ba, haka kuma bai bata amsa ba, Har ta cire rai ta ga ya dan daga hannunsa kadan sannan ya mata alamu da tana iya tafia Sosai ta ji zuciyarta ta sake karye mata, a hankali ta mike ta fito daga dakin nasa tana tafe a hankali a hankali cikin duhu zuciyarta na sake tsintsinkewa har ta karaso kofar AUTA Samun kanta ta yi da kama kofar ta bude ta shiga da salama cen cikin makogwaronta Auta dake saman salaya ta dago a hankali tana kallonta, shafa'i da wuturi ta gabatar tana jan carbi ne, dan haka ta dan zuba mata ido na dan lokaci sannan ta dauke idannuwanta Huznah ta shiga dan kai kawo yatsarta yar karama a cije a bakinta, a hankali ta kasa, kasawa mai tsanani har ta silale ta fashe da kuka tana hade kanta da gwuiwarta A hankali Auta ta shafa fatiha ta mike ta sake zuba mata ido, daga nesan nan tana kallonta, har sai da ta ji ta ringa sasauta kukanta sannan ta bude baki, kasa kasa, da murya mai sanyi irin na mahaifiyarta ta ce" Ki amshi sakinki mana, wannan zama ai bashida anfani ko?" Kanta ta dago da idannuwanta dake zubar da hawaye ta zubawa Auta ido Muryarta na rawa ta ce" Me me ya hanna ki amshi naki sakin bayan naki zaman ya fi nawa rashin anfani?" Auta ta yi dan tsai sai kuma ta juya ta koma saman gadonta da carbinta ta haye tana ja ta lumshe idannuwanta HUZNAH ta karra jan numfashi ta ce" Mijina ne, wanda na ba yardata, nake dakon jiran ya yarda da ni shima, ke ba yarinya karama bace domin kin dauki ciki har ya bare, kuma sarai kin san damuwar yayanki, me zai hanna ki bashi shawarar ya sasauta mana ne? Babu wace yake jin maganarta a duniya irinki, koda kina abu like baki da tunani wani lokacin a haka ya fi yarda da maganarki fiye da ta kowa, yaya zaki ce wai na amshi sakina, dan ba ke bace a wajena? Aure ne ya karra, ta yiwu nice rashin lafiyarsa? Idan haka ne yaya zan yi kennan ni?, Shine zaki ce wai na amshi sakina? Mema na yi maku da zafi ne?" Auta ta bude idannuwanta dake lumshe ta juyo ta zubawa Huznah ido, a hankali ta ce" To ki yi hakuri kin ji?" HUZNAH itama ta zuba mata idon, sai kuma ta dauke, dan sai ta ji ta fara tunanin anya Auta ba lafiyarta kalau ba kuwa? Ture zancen ta yi ta mike ta bar mata dakinta, dan ta kula Auta a duniya ba cika son hayaniya ta yi kwata kwata, bale kwana biyun nan wata nutsuwa ke nuna kanta a tare da ita Washe gari, tunda safiya ta waye yannayin Auta ya fara dawowa irin na da, tunda sako ya sammeta cewa ta shirya zasu koma gida gaba daya take neman ficewa a hayacinta Ta rufe kanta ta yi kula, ta yi kula tsoro da fargaba sun dawo sababi fill a cikin zuciyarta Sai dai tana kan ra'ayinta, da ta sauko ta ba matar nan abinda take nema gwara a wayi gari a ga gawarta, gwara ta mutu a haka nesa da mijinta, gwara ta mutu yayanta da kowa na yi mata kallon mahaukaciya, in sha Allah ba zata daina addu'a da kokarin isarwa da yayanta sakon da take so ya gane dan kankin kansa, in sha Allah ta san wata rana za'a dace, domin sau biyu tana gannin yana yin tsai da tambayarta kamar bata son Fada?......, Tana so ya fahimci ba faɗa bace bata so, abinda ke cikin fadar ne da kansa Da kyar ta iya shiryawa, dan ta san ba jira yake yi ba koda itace kuwa Alkyabarta ta dora a saman suturarta, domin su saka Alkyaba ya zame masu tamkar saka hijab ne, idan babu ita a jikinsune suke jinsu tamkar tsirara Bugawar da akai mata ya sakata mikewa jiki ba karfi ta sake kallon dakin nata ta sauke ajiyar zuciya ta bude ta nufi motar ta shiga itama ta zauna ta hade kanta da abin motar tana kallon kofar da du ake jiran Yayanta ya fito Cike da kamala, tafia t kasaita, jikinsa dauke sutura shiga ta albarka, mai dauke hankali mai matukar daraja, Alkyabarsa mai ratsin golding ce hakama takalminsa irin na saraki mai ratsin golding din ne, kansa dauke da rawaninsa, hannunsa na dama rike da Sandar girma Yanaa fitowa wani bafade daga duke yana gyara rigarsa da kyau, wasu biyu kuwa na rike da lema , daga gefe wani na yi masa barka da fitowa a duken shima hannayensa a jimke yana ta faman yi masa kirari Wajen mai garin garin ya ja ya tsaya wanda ya zube shima cike da farin ciki yana sake gaisar da shi, Mikewar ya yi, domin damar hakan ya bashi da hannunsa Yana mikewa kasa kasa ASADEEK ya ce " Jiya waye ya min allura?" Mai gari ya karra sada kansa cike da girmamawa ya ce" Baban yarona ne Allah ya karra maka lafiya,likita ne ai a cen baban gari ya yi karatun" Kai ya gyada a hankali ya lumshe idannuwansa, ba laifi Allurar ta taimaka masa sosai domin kafin ta fara aiki a jiya ji ya yi kamar zai ci babu, a kasa yake a yashe hannayensa damke da mararsa baya cikin hayacinsa, a dole mafadensa ya kai maganar wajen mai gari, shine suka zo da yaronsa baban likita ne, shinema ke kula da asibitin kauyen ya duba sarkin, nan ya fice da sauri a motarsa ya fita ya shiga gari a daren nan da balakin gudu ya je ya samo allurar ya dawo ya yi masa a lokacin fadawansa sun gama rikicewa harda mai kuka, sun kama da kyar sun mayar da shi saman gado Bayan allurar ne ya samu barci , wahalalen barci mai cike da mafarkai, A hankali Mai gari ya karra sada kansa, muryarsa a mutunce, a tausashe ya ce" Yama ce da zai samu ganawa da kai, akoy mahinmiyar maganar da ya dace ya sanar maka, sai nace sai na tambayi izini" ASADEEK ya karra cira kansa yana bin mutanen da suke ta jifansa da kallo da dago hannu, wasu muryoyin na faman ambaton UMUGHLUK ITIBEL, sannan ya sake duban mai garinsu A hankali ya furta" Ka sanar da shi, abinda yake son fada na sani ba yau ba, idan shi yanada wani maganin da zai karra kashe min cutar ina maraba da haka, idan babu, ka sanar masa cewa Haka Allah ya hukunta" Mai gari ya dago ya dan zubawa fuskar ASADEEK ido,.duda rawaninsa ya tare komai, ama idannuwansa da girarakinsa na fili, ko a yanzu idannuwansa jansu ya wuce misali, haka kuma girarsa a hade take alamu ne na ransa a bace yake Kai ya sada, shi kam da zai bashi dama da ya gwada nema masa magani, irin na hausa na gida, to matsalar tsoro yake kar aje ba zai yarda da magungunnan nan ba, kar yace ba kyau, ama wannan matsalar ai ga dukkan alamu samu ne, shiga gaba ne, tunda karara a jiya ya fahimci matsalarsa, kuma a halin jigatuwa muryarsa na fitar da magana a ciciren da ya dan fahimci wani abin, sai dai ba zai yi gigin kawo masa maganar ba, sai ya karra sada kansa a tausashe ya ce" Allah ya baka lafiya ANNEMOKAL ITIBEL" Kai ya gyada a hankali ya juya dan nufar motar da zai shiga, Daga dab nesa kadan da motar ya tsaya yana hangen Huznah da Auta Huznah kallonsa take yi, irin kallon da ta saba koda yaushe, idannuwanta dauke da bege da girmamawa,du irin turetan da ya yi a hankali ya hango murmushinta sannan ya hango jimke hannunta, irin tana mai aiko masa da gaisuwa, yana sane da zuwanta da safe bata samu ganninsa ba Kai ya dan gyada a hankali sannan ya dan sada dubansa alamun ya mayar mata da gaisuwar itama, sannan ya sake kure fuskar Auta da ido Yannayinta ya saka shi jin jikinsa ya karra mutuwa, a nutse ya cire dubansa ya karasa wajen da aka bude masa mota ake jira Yana karasowa aka shiga gyara masa rigarsa har ya shige ya gyara zamansa aka gyara rigarsa aka tsaya da jiran umarninsa na a rufe a dauki hanya Motar dake gabansa wace Auta ke ciki ta fi daukan hankalinsa, hakan ya sa a hankali ya dan yi alamun zai yi magana Sosai bafadensa ya kawo kunnensa yana sauraro A takaice ya furta" Fatima ta dawo nan" Kasa bafaden ya kara dukawa yana fadin" An gama" sannan ya je ya sanar aka bude mata ta fito ta karaso da dan sauri tana dan sakin fuskarta kadan Shiga ta yi gefe aka rufe sannan ya bada damar a tayar su tafi Sai da suka dauki hanya sosai, a hankali ya rike hannun Auta yana kallonta, muryarsa a nutse ya ce" Menene?, Bakya so mu je gidan ne?" Auta ta kalle shi, a hankali ta shagwagwabe fuskarta, irin wannan kulawar sai idan Umma bata kusa take samu, idan tana kusa komai tarewa take yi , komai Idannuwanta ta lumshe hawayenta suka zubo, hakan ya saka shi sauke ajiyar zuciya ya dan jimke hannunta sannan ya mayar da dubansa bakin titi, Bai san yaya zai kwatanta irin raunin da jarabawar kanwarsa ke hadasa masa ba, Kanantarta, da innocense dinta na matukar saka shi a hali na tunani, uwa uba yakan rasa me take so, me take so ne a duniya? Mutuwa ai dole ce, itama zata mutu fa, ya dace ta yi hakuri shekara nawa da rasa iyayensu? Ama Auta ta kasa yin hakuri, shi kuma ba zai mikata wajen mijinta a irin wannan halin ba, a wajen mijin natama idan ta koma koda yaushe maganarta shine, bata da aiki sai tambayar ko yaya yake? Ita a kaita wajenshi kar wani abu ya same shi, idan aka kawotan an yi ta tambayarta mafarkai take yi ne wani abu ya same shi ko mene? Amsarta daya ce ba komai.....Yana rokon Allah ya sako hasle a cikin duhun dake tare da lamarin Kusan sallar La'asar suka karaso har fada, domin kafin su shigo sai da ya yi ta fama da jama'a, duda yau ba wani lafiyar kirki ne da shi ba, gaisuwarma sama sama yake amsawa, ama sai da ya fan tsaya yana dan amsa murnar karra aurensa, a ransa kuwa yana ayana' karin aure......karin yar matsala dai' A lokacin da suka sauka a falonsa, bayan an gama gaisawa, su Umma du sun zagaye su, Auta na like da shi irin abin nan na da wanda a kwana biyun nan sam bata yi ba, Umma ta dube shi tana murmushi da son cusawa matarsa haushi da kuma sin fara shinfida yarda tsakaninsa da amaryarsa ta ce" Yarona, lalle wannan biki shi ake kira tuwona maina, yar manya ce yarinyar, ba zaka ji kamar a aljana kake ba sai ka ganta, masha Allah ga ladabi, ga biyaya, ga salihanci a wajenta kamar kamar me, ka san meye ga kyauta, tana son talakawanka, masu tarbe sarkar zinarin nan ta basu da awarwarayen gaba daya, baka ga yadda talakawa suka dauketa ba, kwananta daya tak a fadar nan haka ake layin zuwa gaisheta, sai da na takatar dan kar ta kwashi gajiyar da zata kasa gaisheka yadda ya dace" Dan dagowa ya yi bayan ya gama tofawa Auta addu'a a yatsarta karama ya dan kalli Umma Dan murmushi ya sakar mata bai ce Um ba, bare um um, sannan bai kalli HUZNAH bama bale abin ya tsaye masa a rai Umma ta yi murmushi ta karra yin wata yar dariya tana sake satar kallon Huznah ta ce" Yanzu haka, tun kafin magariba aka gama shiryata, kanshi irin na ƴaƴan tubawa ke wasa a tufafinta...., Iso kawai take jira dan ta zo ta gaisheka" Auta ta kara lafewa dam a jikinsa , tana dan karra rike alkyabarsa da hannunta dan bata so ya tashi ya barta da Umma, matarsa kuwa shi kawai take kallo tana ta dannar zuciyarta da addu'a Wannan karron bai dago din ba ya ce" TA JIRA" Daga haka ya shiga kokarin tashi, zurbat Auta ta tashi tana cicira ido da kallonsa Gefen fuskarta ya shafa kadan ya ce" Kin sha maganinki kuwa?" Auta ta gyada kai da sauri, dan haka ya sake yin murmushi ya ce" To ki je wajen umanki kin ji? Tun dazu tana maki oyoyo kin shareta?, Ki tafi ta raka ki dakinki ta maki addu'a, kema ki yi kin ji autana?" Kai ta sada, ta dane kukanta, a hankali ta ce" To Abah" Murmushi ya yi ya juya yana fadin" Allah ya tashe mu lafia" Umma kadai ta iya binsa da iya yin da ta saba da adu'o'in da ta saba masa har ya shige sannan ta juyo da wani irin murmushi a lokacin da Auta ta yi wufff ta fita , HUZNAH kuwa na kokarin ficewar itama Dan takowa ta yi kasa kasa sosai ta ce" Sannu da rashin sannin ciwon kai, na ga harda kokari aka yiwa kishiya, sai dai ta bayar dan inaga bata yarda da ke ba, domin ko sakawa bata yi a wuyanta ba, gashi ita din shi yace yana so kin ga bambancin da nisa sosai" Du irin tsoro, da shayin Umma da take yi takan mayar mata da magana, dan hakane yauma ta dan gyara rufarta ta ce" Hakane Umma, na ga soyaya , domin tsabar so din nema ya saka shi zumudin karbarta a yau" Tana gama fadi ta fice da sauri itama tana fatan Allah ya sa kar ta biyota Umma kuwa kwarai ta shaka , hakan ya sakata yin kasakai da mamaki, Kai ta gyada tana cije lebe a ranta ta ayana' *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣6️⃣ A ranta ta ayana' Yaro man kaza, lalle ina sake da lamarinki, ama ke na zan tabaki da kaina ba, radadin kishi da abinfa zai samu Mijinki zai saka ki dabawa kanki wula da kanki ki kashe kanki, domin kima na san kina masa so irin mai tsananin nan, wannan kam ba algus a ciki, hakan zai kaiki ga halaka wawuya!' Ficewa ta yi ta nufi Bangaren NADIRAH Tana shiha wani kanshin turaren ne ya sake dakar mata hanci, Ita fa mamaki take yi na NADIRAH da innarta, irin yadda suke ba tsafta da kanshi mahinmanci sai ido ya gani, Da safe da ta shigo da sasafe Nadirar ta tardo yana guga, sai da ta tsorata walahi, domin a lokacin kowa na iya shigowa, idan aka tardota tana guga me kennan?, Da kyar ta iya hannata, haka dazu da za'ai mata kwaliyar tarbansa da kyar ta amince domin cewa ta yi bata son hoda da da shafe shafen nan na fusla, a bar mata fuskarta naturel, sai da suka yi mata a taro a taro sannan ta amince, an dauki lokaci ana kwaliyar, hala suturar da aka ciro mata abin sai wanda ya gani, du a burin Umma ta jefi tsuntsu biyu da jifa daya ne, watau ta sakawa ASADEEK yarinyar a rai farat daya, sannan ta kayar da gaban HUZNAH, bayan ta yiwa NADIRAH hudubar du jaraba kar ta yarda ta kwana a bangarensa, bata san tana fada NADIRAH na ayanna nata abubuwa a zuciyarta bane , kala daban daban wa'inda da kunnuwanta zasu jiyo mata da tana iya summa dan firgita da tsorata Karasowa ta yi falon tana yiwa bayin dake zaune a dan takure alamun su tafi, Da sauri suka karra dukawa suka yiwa NADIRAH da inna salama suka tafi zulatansu cike da mamakin hira fa Take yi masu su bayi? Zaunawa Umma ta yi tana karra cika fuska rai a bace ta ce" Ba zai samu ganninki yau ba, yana tare da gajiya ne sai ya huta wai" Wata irin boyayiyar ajiyar zuciya ta farin ciki NADIRAH ta sauke A bayane kuwa ta talwakwabe fuska ta irin mugun hade fuskar nan bata ce komai ba Umma ta sake yatsina fuska ta ce" Ama ya yiwa kansa asara, na tabata da ya yi arba da ke a yau da sai ya mance wanene shi, du takamarsa da mulki da kyau kuwa" Da mamaki HINDU ta kalleta, sai dai bata ce komai ba ta cira kanta a ranta tana ayana' Toh Fah' A fili kuwa ta ce" Ai ba zamu gajiya ba in sha Allah, mu da muke so? Dole mu jure har mu kai ga ci" Ua ta yi murmushi ta kalli HINDU, a ranta ta ayana' shi yasa nake jin ba zan bari ki tafi ba, dan na kula kece ky din bude kwakwaluwar yarinyar nan, dan alamunta tanada ra'ayinta, ama kamar kin isa da ita' A fili kuwa ta mike tana sake sakarwa da NADIRAH murmushi ta ce" Ki huta lafiya, da safe in sh Allah za'a kuma zo a shirya ki, dan kin san kishiyarki na kusa, ko dan ta saka maki ido tana iya shigowa, duda ke ya dace ki fara zuwa ki gaisheta ama ba zaki je ba, kwa hade a cen fadar uban gidanku ku goga, kin fi karfinta walahi, sai da safe idan na samu damar kaiki zan zo ko na turo yam mata" HINDU ce kawai ta iya amsawa, NADIRAH ta cika, iya cika, a zuciyarta kuwa fadi take yi' Aikin banza, idam an samu damar a kaini?, Hehehe an fada masa cewa na yi ina son zuwa na gaishe shi ne? Wai takamarsa kyau, wani kyan mutumen da ya haifi su Innar birni da innata? Sunna ce masa Baba?, Ai sai fatiha kawai koda an yi kyan a da, a yanzu an tsufa kuma sai hakuri, oh ta yiwu matarsa fa kishinshi take yi, itama ko yarinyar ce ko tsohuwa ce? Allah dai ya tsareni da cusa kai ki ta Aminu!' Tana Fita Hindu ta rafka tagumi, sai kuma ta saki hannunta ta ce" Allah, Allah mun tuba Allah, kana zamanka sai shedan ya ringa sako maka tunani kala kala, kim ga kawai sai ta ringa min ka.da kwartaye matar nan" NADIRAH ta kalleta a zabure tana rufe baki ta ce " Astagfrulah Inna mamansa ce fa aka ce, ni mamakin da nake mamansa wace ta haife shi ko kanwar mamansa?" "Ke hadimarsa ce, ni da Sarki ya samo min labari sala sala, baki ga jiya har dare muka raba muna tataunawa ba? Kina ji ita wannan a da baiwa ce, irin bauta ta da suka yi wace ba'a biyansuma, kuma da kika ganta a nan kina ji irin aminiyar nan ta kuryar daka mahaifiyarsa ce, domin baiwa ce da ta zama kamar yar uwa, ita ta raine shi, da kanwarsa shi yasa suke ce mata Umma, ba wata mahaifiyarsa, ke yanzu mahaifiyarsa zata neme shi da mugun nufi? Ki duba fa kalamanta, ni abinda nake son ganewa daya me tak da matar nan, shin asiri akai mata ko nuna mata aka yi idan bata yi ba za'a kasheta ko wani nata sosai? In ba wannan ba gaba daya matar nan gaskiya ko shedan dan makarantarta ne, Indi wai bata maki kama da lwartaye?" HINDU ta karashe tana karta kama haba da zarro ido Da sauri Indi ta mike tana cire alkyabar nan ta kuma warware gashinta ta cuje dan kwalin ta ce" Wa bilahilazi ki yi bakinki ya fita innata a kashe mu kafin mu yi ceton bale na komawa Aminun, Astagfrulahi ina ita ina kwartanci jama'a tsofai tsofai da ita, Umansu ce fa, ai ba zata fara ba Innata, bara na wanke abin nan kaikayi yake min a fuska bama na gani da kyau na zo mu yi carafken nan, jiya a tara na fadi ba manta ba" Da ido innarta ta rakata, sai kuma ta sauko kasa tana cire daurin da aka kafa mata itama ta rafka tagumi a bayane ta ce" Oh ni ta Habu na shiga uku yar nan tana tune da shegen nan wuya uwa marikin lema?, In sha Allahu Indi ba ke ba Aminu, yau dai da gani ga UMUGHLUK ITIBEL?, Kai jama'a da babu abinda zai hannani fashewa da kuka, yo ni ai Adu'a nake yi kar na fada masa su waye mu mu shiga uku, Je ki dawo mu yi carafken ko na manta wannan tunani na matar nan kamar kwartuwa, dan nima ji nake yi kamar na yi sabo walahi, mace baba haka ina ita ina irin aikin nan?, Kawai itama tana magana ne tana lumshe lumshe ga wasu idannuwa kamar maya sai ta kureka da kallo, in ba wannan ba ai.na za'a yi mata wannan tunani ba sam, sai kuma wasu magangannu dai irin na yan iska, ama in sha Allahu inaga ba zata kasance kwartuwa ba sam, ai ko dan gudun kar danta ya karta zata kiyaye ai ba kyau kwartanci ".............( Allah dai ya taro ki Hindu madam) __________________________________ Washe gari haka aka tashi da baki, kamar koda yaushe, sai dai na yau manya manyan baki ne dan yi masa barka da sabon aurensa, Haka ya wuni amsar bakin har yama ta yi ya kowa ciki dan samun dan hutu kafin lokacin sallar magariba ta yi A irin lokacin ne kuma ya sake samun wani lamarin na matan uku dake rayuwarsa, wani zaman, da wani shirin daban, domin da gaske Umma ta dage sai matar da aka daura masa ta zo ta gaishe shi, hakan ya sa ta ki zuwa kawota danma kar su dawo su tardo ya shige barci, sai kawai ta tura Baiwa cewar maza a rakota , idan ta fito jakadiya ta yi jagora a rakota Sosai HUZNAH ta karra kimtsa zamanta, Auta kuwa ta bude litafinta tana nuna masa cewa zata bashi hardar wata Adu'a da ya koya mata a kauye Baiwar ta samu shiga falon domin sakon UMUGHLUK ITIBEL ne Tana shiga NADIRAH ta fito daga kicin, hannayenta sanye da safar hannu, kugunta daure da abin girki, girki suke yi ita da innarta, fuskarta da kwaliyar da akai mata, ama ta cire tufafin ta mayar ta ninke , gashinta a baje yake a bayanta, girki suke gwadawa ire iren WA'INDA masu gyaran nan suka koya mata Har kasa Baiwar ta duka, kanta a kasa, domun ta tabata matar nan ko wacece ta jikin sarauniyarsu ce Kanta a kasa ta gaisheta NADIRAH ta amsa tana sake gyara daurin abin girkinta a kugunta Baiwar ta sake sada kanta ta ce" Allah ya taimakeki, sako ne wajen sarauniyarmu, daga Umma uwar bayi, aka ce ta fito mu mata jagora baban Falo, a irin wannan lokacin UMUGHLUK ITIBEL na nan zai amshi gaisuwarta" NADIRAH ta yi tsai tana ta kallonta, a hankali ta fahimci me sakon yake nufi, watau ana nufin ta je ta gaishe da shi babansun? Baki ta yatsine tana dan waigawa dan bata so Innarta ta ji, domin a wannan lokacin da take jin zumudin su fitar da gashin cen ta dangwali romonsa ta zira a bakinta babu abinda zai sakata wanka ko cenza kaya da zuwa shirmen gaisuwa, wai inama ruwansu da sai ta gaishe shi ne? Su shafa mata lafiya, ko haka ake yiwa matan safakan ne? Dole sai an san ka je wajen miji? Shi yasa a sarauta bata ga komai ba sai tsabar wauta da rashin sakewa Hankali kwonce NADIRAH ta ce" Idan kin je ki ce, na ce yanzu ina kicin, sai dai wani jikon" A zabure baiwar ta dago, ba da gangan ba ta yiwa Nadirah kallon tsaf, a rashin gane me NADIRAH ke nufi ta ce" Sakon na sarauniyarmu ne ranki ya dade, sannan sakon daga UMUGHLUK ITIBEL ya fito, domin idan UMMA tace, shi yace" NADIRAH ta saki lalausan murmushi tana gyara tsayuwarta ta ce" To dada, inaga a nan dai kice kawai matarsa a sanina, sai innata, idan kuwa ita zan kira maki toh sai naje aikar" Da sauri ta sada kanta, wata zufa na neman karyo mata, ta sake sada kan nata a hankali ta furta" Allah ya huci zuciyarki, Allah ya karra girma, Allah ya karra daraja Sarauniyarmu, In sha Allah zan isar da sakon, A gama lafiya" NADIRAH na tsaye tana kallon ikon Allah har matar ta fice kamar zata kifa Ido ta kikifta kasa kasa ta ce" Allah mai alkhairi" Daga nan ta koma tana yiwa Innarta hira wace ta yi bake bake a wajen Four tana jira abinda suka saka ya gasu su ciro Tunda ta shigo har falo dan Umma ta bata damar shigowar a tunaninta tare suke da NADIRAH ta zube kasa, kanta a kasa ta kasa fadar sakon da ta gumtso a bakinta, domun har jikinta rawa yake yi a lokacin da ta fahimci kwarai da gaske ZAKIN SARAKAI na zaune Umma da dan takaici ta ce" Ki fadi sakon mana kin tsugunna a waje kin mana shiru bayan kin ga ke ake jira?" Kai ta sake dukarwa kamar zata kifu, muryarya a raunane kamar zata fashe da kuka ta ce" Allah ya taimakeki, sako daga sarauniyarmu, tace ace girki take yi, sai dai wani jikon" Ba Umma ba, harta UMUGHLUK dake dan kallon Huznah sai da ya yi dan tsai , uwa Uba UMMA da ta kallota a zabure, hakama HUZNAH da sai da ta kusan mikewa dan tsorata, a gangaro kan Auta da ta dago tana zarro idannuwa kamar zasu fado tana kallon Baiwar, wace tuni take share hawaye, hawaye na tsoro, domun an hore su da fadin gaskiya, bale irin wannan dole zasu sanar da abinda suka gumtso, sai gashi, sai gashi ta gumtso mai karfi, kuma Umma ta saka ta fada a gabam Uban gidansu baki daya Umma har hade harshenta take yi wajen fadin" Rufe min baki, wannan wace irin magana kike yi haka?, Na tabata wannan sako ba daga ita ya zo ba, waye zai shige kasam rigarta ya bata mata sunna run kafin ta ga mijinta? Na tabata wannan sako an yi shi ne dan a hadata da UMUGHLUK ITIBEL, maza ki tashi ki rakani wajen wace ta baki wannan sako, ko wacece na ganta, domin na tabata ba dai Sarauniyarmu ba!, Kuma ko waye a bayan haka zai bayana ne!" Shi ihun da Umma ya fi damunsa, haka kuma kafin ya yi wani abu har Ummar ta fice kamar zata kifa Juyowa ya yi zai yi magana dan HUZNAH a tsaye take itama , da niyar umartarta ta zauna sia ya ga wani murmushi ya kubuce daga fuskar Auta Dan kallonta ya yi, sai ya samu kansa da yin murmushin shima Muryar HUZNAH ce ta dakatar da shi a lokacin da ta duka kanta a kasa ta ce" Allah ya huci zuciyarka, na tabata da wani abin daban, ta yiwu bata gane sakon daga nan ya fito ba, bayan wannan me hadinta da kicin? Sam sakon ba naka bane" Ido ya dan sake kura mata , haka kawai ya samu kansa da tunanin toh daga ina sako ya same shi haka? A masarautar nan? Ko daga wata masarauta, komai rashin da'ar Yar sarki ko matarsa, ba zasu turo da sako haka ba gaskiya, ta yiwu bata gane din bane, ko kuma ba ita aka ba sakon ba, shi abinda yake dan bashi mamakima shine, bata gane waye aka aura mata bane? Ko an mata nasihar zumudi ne? Dan kwarai ya yi tunanin a kofa zai tardota tana binsa da kallon nan kamar na mahaukata, sai gashi shiru Murmushi ya sakarwa matarsa, hakan ya sakata suake ajiyar zuciya, domin damuwa ta sameta kar ransa ya bace abin ya shafe su baki daya, domin ba zata iya tuna bacin ransa ba, bata so, bata son tunawa, bata ga da kyau ba ko kadan, a ranar da ya yi bacin rai mai sunna bacin rai? Bata ga da kyau ba ita da kanta, bale wa'inda le zagaye da su ___________________________________ A haukace Umma ta shigo, bayan ta dakatar da Baiwar da ta tabatar mata nan ta shigi ta kuma kwatanta mata wace ta gani Hankali tashe, rai bace ta dubi Inna dake rauda kai tana kallon TV ta zabura jin budewar da shigowar ta ce" Ashe bata da hankali? Ta san da wace irin wuta take son yin wasa? A tarihin rayuwata ko a zamanin iyayensa ban taba gannin an bashi amsa kai tsaye irin haka ba, hala bata da hankali da zata ce a cewa UMUGHLUK ITIBEL tana kicin ba zata samu zuwa gaishe shi ba sai wani jikon?" Daga saman kujera sai da HINDU ta fado kasa warwas sannan ta dabi kai kamar mai shirin tayar da aljannu ta ce" Lah ha ila ha ilalahu muhamadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallam, wani shegen rikaken dan iskan makaryacin ne ya gilawa Indi karyar nan? Allah na tuba yar da ko fitowa bata yi ba muna ciki muna dahuwa? Ka ga shari irin na masharanta, in itace a yau a yanzu yanzu in zama wancen TVn a ringa jona ni dan Annab............." "Innata" Indi ta fada da dan karfi tana zarro ido dan gaskiya ba zata iya yin shiru innarta ta yi rantsuwar alkaba'i a kan gaskiya ba, Ido ta ribga kikiftawa, hakan ya saka HINDU yin wuki wuki murya a raunane ta ce" ki bari na karasa rantsuwar nan kin ji yar indi? Ai ba kina nufin na yi shiru bane ko?, Ba zaki aikata haka wa babanmu ba ai ko?" Indi ta yi shiru tana murza hannunta, sai kuma ta ce" Gani na yi muna girki a lokacin ne innata" "Karbi nan, na ce dambulaninki Indi zo nan dan ubanki na gagaura make mari, so kike a shake mu muna ihu har mu daina? Zo nan" HINDU ta fada tana rarumar abu ta mike dan ta shako Yar........... Mun shiga uku☹️☹️☹️☹️ *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣7️⃣ Ba edditing NADIRAH ta yi tsuru tana kallon Innarta, da Umma dake salalami ta kasa tsayuwa a waje daya Innarta ta sake kallon Umma, sannan ta kallo NADIRAH ta ce" Yar gidan Habu makadi ki zo ko na zo?" NADIRAH ta sake shagwagwabe fuskarta ta ce" Innata, gani na yi magariba ta shigo, kafin mu karasa ai ta yiwu kuma ya shiga barci dan ai baba baya jira barci na iya daukansa koda yaushe ko Innata?" Hindu ta karra tafa hannu tana sumurtu, lokaci daya ta dage zanninta ta haura shi saman ciki sannan ta nemi tsalaka kujerar dake tsakaninta da Nadirah Ido NADIRAH ta zarro, ta sake kallon innarta Da gudu NADIRAH ta fala cikin dakinta ta rufo harda saka Ky sannan ta karasa wajen kujera ta zauna tana sauke numfashin gudun da ta sha sannan ta dan tsurawa waje daya ido tana dan balancing din kafafuwanta Samun kanta ta yi da mikewa ta karasa gaban madubi ta dan rankwafa kadan tana daure gashin kanta a baya Dan murmushi ta yi tana girgiza kanta kasa kasa ta ce" Amarya , Amarya ce, koda ta auren dole ce, koda ta karkara ce, in ba abinka ba baban su Inna ai mu mutanen karkara mun fi kowa riko da al'adu, a gida ba mace ke fara zuwa wajen miji ba, koda sarki ne, kasancewarka bako koda wanene kai ba shi zai saka a kwasheni a kaini gaisheka ba....., Duda ba maganar fahimtar junna ko tare yawun tsufa zan yi ba, ama a ji labarin nan a labba ai na fadi ba nauyi, Idan har da rabon mu gaisa zamu gaisa in la zo nan da kanka Babansu" ( kuturu🫢🫢🫢 abinda kike shiryawa kennan? Lalle kin traro match) A falo kuwa zaman dabar Innarta ta yi tana salati tana sanar da ubangiji tana kallon Umma ta rasa me zata ce mata Umma ta dafe kai itama da takaici ta ce" Ta kula, ta ajiye shirme da yarinta da wasan dake dawainiya da ita, ta ringa bambance baba da kuma dan gidan baba, ki fahintar da ita shi din baba ne, ba maganar wargi tsakaninsa da matarsa, ko waye ba zai rainashi ba, koda matarsa ce shi din sarkinta ne!" Hindu sai ta samu kanta da jin maganar wata iri, ko matarsa ce shi din sarkinta ne? Toh mutane, yo ai itama da ta tsorata dan Indi bata riga ta zama matarsa a aikace bane, da hakan ta faru ai tana gannin abu ne daka iya faruwa tsakanin mata da miji ko? Ama yaya Umma ke dan so ta nuna kamar Indi ta yi sabo? Umma ta dora da fadin" Bale a gaban kishiya take, matar da ta ci hakuri ta kora da ruwan zurra ido,matar nan ni na tabata hakurinta zai kasheta wata rana, kin kuma san maza na masifar son macen da sai yadda suka yi da ita ko?" Hindu ta karra yin tsuru, ita Umma na magana ne ira tana aunawa a kankin kanta, Allah ta tuba ita din nan karan kanta maganar ba wata ji take yi ba, tsakaninta da Habu wani lokacin sai ta zo barci take lalabawa ta tashe shi a yi zaman tsakiyar dare a yi magana a yafewa junna, bama idan wata ya raba tsaka ya zama tulelen nan, takan ji komai a fili yake Alkur'an, takan bashi hakuri shi kuma yakan ce in bai yafe mata ba ai shi zai shiga uku dan idan ta tire daga yadda take yanzu ta yiwu a mata sarauniyar makada......., Gaskiya a nan tana iya cewa Umma kamar ta yi daya, wasu mazan ai a lokacin da kika zama sai yadda suka yi da ke din nema suke cin kaniyarki, Allah mun tuba a rayu da tunnanin za'a mutu kawai, in ba shi ba ai har a dambatu da makocin raba gado Umma ta ci gaba da fadin" Mema ya hada fatarta da girki?, Ina ita ina aikin da aka zuba mata bayi dan su yi mata? Wanka kansa bai dace ta yi da kanta ba, ya dace ta dauki girman dake kanta fa, bana son abinda zai zamo tsegumi da tsuguri tsoma a cikin bayi, bana so kuma wancen ta yi tunanin ta samu hanyar da zata iya shiga tsakaninta da UMUGHLUK, uwa uba shi din da kansa idan ya fuskanci akoy maganar raini sai ya tsireta walahi!" A zabure HINDU ta zarro ido , lokaci daya ta ce" In sha Allahu Bama za'a kai cen ba, yanzun ma sharin shedan ne, yar da bata cewa komai? Yar mai tsantsar biyaya? Na tabata rashin fahimta ne, yau zan kwana ina fada mata kuma zata dauka, a yafe mana ba zamu kuma ba" Umma ta tabe baki tana sauke ajiyar zuciya, tabas yarinyar nan kamar ta mata ila ita din da kanta, a tunaninta yau da wata ce daban ta aikata haka ba wace take ji har kasan zuciyarta ba, da bata san abinda zai iya faruwa ba walahi! Juyawa ta yi tana fadin" Zan koma bangarena kafin ya gama sallah na koma na bashi hakuri" Inna ta gyada kai tana kallonta har ta bacewa ganninta Tagumi ta rafka tana sake kiran sunnan yarta da fadin gwara ta bude kofar nan su fuskanci junna , ita kuma ta yi shiru ta ki fitowar, domin a muryar Innarta tana gane bata sauko ba, idan ta sauko sa yi maganar Bayan sallar isha'i da kyar Umma ta samu komawaa domin baki ya yi a irin lokacin, sai dai tama zuwa ta sha mamakin gannin Auta har yanzu bata tashi ba Zama ta yi ta shiga gabatar masa da lamarin ta fuskar rarashi da ban baki, ta karashe da fadin sakon sam na daga wajen sarauniya ya fito ba, wata kula kula ce, in sha Allah tana kan bincike dan ba zata yarda a fara kawo wargi a gaban danta ba Murmushi ya yi yana basar da maganar, sannan yana karra gannin girman Umma a zuciyarsa, domin irin yadda take tsaye a kan lamarinsu ko iyayensa sai hakan, shi fa tausayinta yake ji baiwar Allah, ya tabata yakinta na ta kawo yarinyar cen gabaansa ba komai bame sai dan ta samu yan jikoki abinta, baban mafarkin Ummansu ta ga yan magadan sa, bata san shi bama zai kwatanta wani abu da yarinyar ba bale har ya dauki wani nauyim zuciyar, kai shi koda ya warke gaskiya da wahala ya tara zuri'a da yarinyar, dan sam bai ga tarbiya a tare da ita ba, irin yadda ta nuna din nan a saudiya ta bashi mamaki, bai taba tunanin akoy irin haka a hausa ba, abu kamar rainon arne? Sai da intacen bawansa ya daka mata tsawa fa a lokacin da ta ga dakinsa ido rufe ta nemi kutsawa da neman fado masa a jiki, bata san ba gidan ta samu ba, yanzu da wani lalatacen ne shikenan ta fado gidan sauki zai murjeta son ransa a bagas, ita a tunaninta soyaya ce sai ya bace mata batttt, kai shi yauma zai kunna wayarsa da ya bata layin, dama bai kunna bane saboda so yake ya huta sosai saboda abokan kasuwanci, layinsa ne sanane wa yan kasuwa kadai, Umma ta yi murmushi tana kallon Auta ta ce" Babyna kin yi sallah kuwa?" Auta ta dago a dan tsorace, dama tunda ta ga Ummar hankalinta ya kasa kwonciya ta tabata sai ta mata fadan ba ta hannata jimawa wajen Aba ba Da sauri ta gyada kanta, sai kuma ta bude bakinta dake dan rawa ta ce" Dama harda ce zan yiwa Abah, shine, shine na jima" Umma ta yi gagawar tareta dan karma ya saka wani abu a ransa ta ce" Aa ai karatu ba komai Auta, dama bana so kina jimawar ana ta hira kuma ki je baki samu isasshen barci ba , hakan na taba lafiyarki, idan kin gama yanzun tashi mu tafi na gyara maki komai ki sha maganinki ki kwonta" Auta ta budi baki har tana dan hardewa ta ce" Ummah, ban gama ba, dama so nake na yin, kuma na sha maganin a gaban Aba yanzu ko Aba?" Daga rubuce rubucen da yake ya dan dago ya gyada kansa, sai kuma a takaice ya ce" Zan rakata idan ta yi Umma" Dan zuba masa ido ta yi ta ga hankalinsa ya dauku a abinda yake rubutawa Wani irin harara ta watsawa Auta sannan ta yi kwafa ta mike ta yi masu sai da safe harda jadada a yiwa Auta addu'a fa idan zata kwonta Bayan tafiyar Umma Auta ta jima tana kallon waje daya fuskarta na nuna alamun she is sad Sai kuma ta sake tino maganar dazu Ita abin ne ya sakata dariya ba dan komai ba sai tino maganar mahaifinsu da in dai yan tsokanarsa suka motsa ya kama adabar mhaifiyarsu da maganar kennan, a kan rikicin da suka sha tsakaninsa da ita dan aurwn hadi ne su a lokacin, kuma ita mahaifiyar tasu itace Auta, ya zamto tsaf take cewa ba zata je gaishe shi ba gaskiya ta gaji, shi kuma a lokacin eh lalle an bashi mata ne, ama farat daya ya ji du duniya ta masa iya yi, haka yake sabo babar rigarsa shi ya je ya gaishetan, ko ba komai ai halal ne, to mahaifin nasu ke anfani da haka ya yi ta tsokanar mahaifiyarsu ita kuma tana sinne kai tana dariya, summa sunna shaan dariya da mamakin wai du girman sarauta irin ta mahaifinsu dama zai iya aikata haka? Zai iya tashi da kansa ya tarda iyalinsa? Kwarai so wani abin ne mai girma Kara sakin murmushi mai sauti ta yi, wanda ya saka yayanta dagowa da dan sauri ya tsura mata ido yana dan kallonta da byron dake hannunsa Dariya ta yi har sai da jerarun hakoranta suka bayana sannan ta mike ta koma dan kusa da shi kadan da hannunta ta shiga nunawa ta ce" Abah, kana tune da labarin Papah da Anna?, Papah yace a gaban dogarai da fadawa nake saba babar riga na kai gaisuwa dan idan ta kiya tsaf zata ce ai itama mutun ce kulun kulun sai dai ita ta wani zo ta gaisheni?" Rawanin da bai sauke ba ya samu kansa da yi masa kasa sosai har habarsa ta bayana, Dariyar da kanwarsa ke yi da tsohon tarihin da ta tuno ya daka shi jin kamar numfashi ya masa kadan dan farin ciki A hankali ya saki lalausan murmushi, domun ya gane da me take hada zancen, sai kuma ya dan karra kure fuskarta da ido kasa kasa ya ce" Auta, ita fa ai ba irin na su Aba bane ba fa" Auta ta dafe habarta ta ce " Abah, sakon naan daga wifey dinka ne, Allah ma ko" Ido ya zarro da mamaki ya ce" Noh,kar ki rantse Auta" Auta ta sake sakin yar dariyar da ta saka Yayanta lumshe idannuwansa yana mai godiya ga Allah, uwa uba ya shiga tunnanin kennan akoy sauran dariya irin haka a tare da ita?, Ya Allah kennan tana da sauran tarihi a zuciyarta da kwakwaluwarta? Kennan kanwarsa bata shige cikin duhu gaba dayanta ba da sauranta? Auta ta kara dubansa ta ce" Abah, ka bada dama a kawota gobe sai mu gani ka ji? Please Abahna ni ina soma na ganta plz" Idannuwansa ya kankance, sai kuma ya gyada kai yana murmushi ya ce" Me yasa kika damu haka Auta bayan baki santa bama?" Ya yi tambayar ne dan ya gane idan har ba kanwarsa na neman shakuwa da abar da yake da takaitacen zama da ita a zuciyarsa Auta ta yi murmushi ta ce" Abah, ina son mutun mai karfin zuciya, mai courage, in dai daga ita sakon nan ya fito nima ina saka ran wata rana na yi karfin zuciyarta, Abah Kaine UMUGHLUK ITIBEL sunnan da talaka ya baka , kuma sarakai suka amsa, ba kai ka sakawa kanka dan isa da fin karfi ba, du wanda ya aiko maka da sakon nan, ko ita, ko ba ita ba i swear ina son ganninsa Abahna" Murmushi ya yi shima, sosai mamakinta na neman hanna shi yin abinda yake yi, Idan har zai tuna rabonsa da gannin haka daga Auta gaskiya an jima, irin mugun jimawar nan, murmushinta kansa sai a jima bata yi ba, bale dariya? Kai ko hira ake yi sai ka ga kamar bata san me ake cewa ba, ashe tana iya doguwar magana har haka hankali Kwonce?, Shima sai ya samu kansa da son yi mata abinda take so din, dan haka cikin nutsuwa ya ce" Ohk ohk, zaki gani yarinya da ba ita ta bada sakon nan ba, zaki gani, ama ba gobe ba, gobe da jibi inada zama a fadamai tsanani, inada Shari'a masu tsaurin gaske da rikici a ciki, in sha Allah ranar asabar alhamis sai mi zauna one 12 mu ci abinci tare?" Da farin ciki Auta ta amsa har ta karra bashi wani mamakin ta ce" zaka cire Rawaninka?" Da mamaki ya dubeta ya ce " *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣8️⃣ Da mamaki ya dubeta ya ce" Me ya kawo maganar cire rawani kuma?" Auta ta shagwabe fuska ta ce" Please Abah, idan ka yi haka zan ji dadi sosai fa?" Murmushi ya yi ya mike yana fadin" Oya maza miko ki yi hardar na raka ki dare na yi fa" Ajiyar zuciya ta sauke ta dauko ta mika masa sannan ta gabatar masa da hardar shi kuwa yana sauraronta har ta gama Yana murmushi ya nuna mata hanyar da zasu bi ya rakatan sannan suka dauki hanya Har suka karasa kowane na tunani a zuciyarsa Shi yana mai karra godewa Allah da tunanin ai idan hakaa ta ci gaba da samuwa tsaf zai mayar da ita wajen mijinta, sauki ya samu Masha Allah, dama a gaban Umma ta yi hirar nan a sake, da Umma ta ji dadi aa ranta Auta kuwa sunna tafe tana tunani kamar haka' shikenan kai ba zaka bude fuska ba sai kaa yarda da mutun? Na ga ai itama matarka ce, maganar yarda kuma ai ya kare ko?, Abah ban santa ba, hasalima ian tsoron iyayenta domin nice kat cewa summa da wani saka hannunsu a lamarinka, amaa haka kawai tunda akaa ce an daura aurenku nske zumudin son ganninta, ko dan zamu karru ne a cikin duniyarka? Ko dan zan kara samun wata yar uwar ne bayan HUZNAH, sam ba wai ina sonta dan na kuntatawa Huznah bane, ko daya, hasalima HUZNAH ni babu abinda ta min, yannayin mu'amalarmu ne haka, wani lokacin har hira muke yi fa, ama da wata zata karu cikinmu sai nake jin farin ciki sosai, sai maganar da aka fada , na tabata bayin masarautarmu ba dai maganar su ringa kawo karya ba, wannan Umma bata samu galaba a kansu ta wannan fannin ba, du inda maganar nan ta fitoz da tushenta, tushsen nake son gani ni kuma' Har kofar dakinta ya rakata sannan ya koma ta hanyar da suka biyo bangarensa ya ci gaba da aikinsa yana sake rubuta hukunce hukunce ne na sata, da zina, uwa uba Luwadi .......................shara'ar dake gabansa mai zafi ce, kuma mai cakulewa ce, a dole Sheikh ya kawo masa su dan shi kadai ya isa ya tsaya ido cikin ido ya zartar kuma a bi koda ba'a sallah! A ranar HINDU bata zauna da yarta ba sai washe gari, tana tsakar yi mata nasiha Kira ya shigo a wayarsu Tana gannin yayarta ce ta tashi tana murmushi ta shige ciki dan su yi sirri FADIME a sanyaye ta ce" Hindu kin kaura ba?" HINDU ta yi shiru FADIME ta ce" Ki tataro ki dawo dakinki kin ji abinda na fada maki, kina nan ko bakya nan abinda Allah ya nufa zai samu yarki sai ya sameta, kar ki yi wasa da aurenki mana" HINDU ta gyara zama ta ce" Aunty ba wasa nake yi da auren ba, dama dan Habu baya nan ne, kuma kin ga jiya dai Indi cewa ta yi a cewa UMUGHLUK sai wani jikon zata je gaishe shi" Ai kuwa rikicewar da Fadime din ta yi har ta zarce ta HINDU, haka take salalami itama ta saka aka ba NADIRAH wayar, kamar zata fito ta wayar haka take yi, fadi take tana maimaitawa cewa Babansu ne fa, a kan me zata yi aiki kamar na yar kwaya? Tsaf suka karra sileta, ita kuma ta yi shiru, dan a ranta ayanawa take yi' Ba ku gane komai bama yaya da kanwarta gaskiya, ni ba zan fara kai kaina ba fa, yo ai ba haka ake yi ba'! Haka suka wuni sunna yan abubuwansu dan debe kewa, sai dai kowace zaman dakan ya fara isarta, domin ba sabawa suka yi ba gaba dayansu A haka har kwanaki biyun suka shige, a ranar na ukun ne sabuwar maganar zuwa bangarensa ta karra tashi, wannan karron kam ta ga da gasken gaske suke, Tun karfe goma aka shiryata akace cin abincin rana a bangarensa Kwata kwata sai ta ga abin nan ba wani tsari sai shirme Bata dai ce komai ba , haka ta zuba ido tana bin motsin kowa har lokacin ya yi aka rufa mata wata mahaukaciyar alkyabar da ita da kanta sai da ta ringa shafata, domin har ga Allah ba dai laushi daa kyau ba A nutse aka bude hanyar baya domin rana ne gatse gatse da nufin bi ta bayan da ita, Sun dauko tafia su hudu Umma sai karra gyarata take yi tana sake gyara mata rufarta ta ja ta tsaya A hankali ta nemi dukewa, hakan ya saka jakadiya tareta da sauri ana faman ambaton Allah da yi mata sannu Ido rintse ta kwashi barin jikin karya kab kab kab kamar da gaske Hankalin Umma tashe take talabota tana tambayar menene? Lafiya? Ama NADIRAH ta kasa fadin komai Hankali tashe Umma ta sake dagota tana girgizata ta ambaci sunnanta tana tambayarta menene? Muryarta na rawa ta furta" Umma, bayi nake son shiga, innalilahi zai bale" Har ga Allah Umma ta yarda, haka kuma da mahaukacin gudu ta saka aka juya da NADIRAH aka nufi ciki da ita hankali tashe aka nufi dakinta da ita Inna naa tambayar lafiya? Bayin ta shige bayan ta watso alkyabar ta ja ta rufe ta haye saman abin aikin ta ringa jan ruwan tana kakari kamar wace ke aikata aikin da ba jira😌 A waje Umma da inna ke kai kawo ana tambayarta yaya da sauki? Tana buga gyaran murya Umma ta dubi Inna hankali tashe ta ce" Sai fa mun yi da gaske, kar aje kishiyar ke son cin mata, kina ga haduwa ta gagara bayan an daura aure ba yau ba?, Kar fa aje mun raina wayonta ita tana mana kallon shashashu, kar aje wankin hula ya kaimu dare, kar aje ta san me muke shiryawa tana neman yi mana sakiyar da ba ruwa, ina zuwa zan je na sanar masu abinda yake faruwa sannan na fita da kaina na kawo jikakun karya tambaya da kaikayi koma kan mashekiya, ko me ta aikata mata sai dai ya koma kanta walahi, wannan wace irin masifa ce, ki duba ki ga kwaliyar da yarinyar nan ta sha fa? Ai karya take idan takamarta bokaye ni a hanya na kwana dan ubanta!" Inna na tsaye bayan fitar Umma ta samu kanta da zaunawa tana kallon kofar bayi, haka kawai sai take jin damuwar rashin lafiyar da kuma rashin yarda idan har Indi bata da lafiyar ne, koda yake shi gudawa ai kawai zuwa yake yi kai tsaye, bara ta samo kuka ta bata ta sha sai ya tsaya, wannan abu dai kam itama bara idan ta bata kukar ta tofeta, idan har aka yiwa UMUGHLUK ITIBEL da NADIRAH faraku ai ita ta shiga uku, ko haduwa ba zasu yi ba kennan? Firgit ta mike ta fice itama ta rufo dakin ta tafi neman kuka a wajen kicin din bayi, ta tabata ba za'a rasa ba __________________________________ Kasancewar har sha biyun ta gota ya zamto shima ya sauko dan cin abincin Shigarsa ta sababin kaya ne kamar yadda ya saba, rawaninsa wanda aka rufe fuskarsa gaba daya ne Tun daga Auta har Huznah sun sha kwaliyar da sai da suka birge shi Sai dai mamakinsa gannin bai tardo harda yar mulkin a wajen ba Sakon da Umma ke sanar masa ya saka shi dora dubansa a kan Auta, wace yana kallonta ya hangi boyayiyar dariya a fuskarta Samun kansa ya yi da mamaki mai tsanani da kuma jin haushi hadi da son gaskatawa A kausashe ya ce" Karfe takwas na dare ya mata a falon nan, koda tana tafe ana tare abinda ke damunta ne!" Daga nan ya mike ya fice, domin bama zai ci abincin ba, ikon Allah shi za'a rainawa wayo? To ita me take takama da shi da har zata aikata haka?, Idan tunani take yi akoy maganar soyaya ko makamanciyarta da zara saka ya fuskanci me take nufi ta makaro!, Ba zai dauki rainin wayo ba sam!, Zara zo zai kuma fada mata gaba da gaba! Jikin Umma ya yi sanyi ainun, ba dan komai ba sai dan sanin da ta yi dole ne Nadirah ta zo koda ana tare mata gudawar kuwa, ita da ta so ta shigo kanta a sama? Ita da ta so idan ta zo sai hankalin kowa ya tashi? Akoy matsala Daga nan bangaren Nadirar ta koma dole, a lokacin Innar Nadirah ta dawo tuni ta tarar da Nadirah kwonce a dakinta tana rera wakar dandali tan kada kai, bayin ta shiga da sauri, ai kuwa bata ji alamu ko gannin alamu na abu mai doyi ya sauka ba, a lokacin ne ta yanke hukuncin lalle sai sun fuskanci junna ita da y'arta, sun yi magana ta fahimta Abinda Nadirar ta fada cewa ai ba aji ne ya sakata rushewa da kuka sai da Nadirar ta ringa rarafe tana bata hakuri da rike kafarta sannan ta saurareta, ta gama yanka mata kashedi ta fito Umma ta dawo Fuska da alhini Umma ta sanarwa Inna umarnin UMUGHLUK ITIBEL HINDU ta ce" In sha Allah zata kasance a wajen a lokacin, kar ki damu Umma" Da wannan Umma ta fice dan zuwa ta amso su karya tambayar nan dan ba zata yarda a cinma yarinyar ba! ( Uhum, hakane, wani lokacin makashin naka ke baka kariya kuma cikin kudurar ubangiji) _____________________________________ "Sannu, kar ki fadi mana" Muryar Umma ke fada kasa kasa tana karra shakar kanshin tutaran yarinyar domin ita ke rike da ita a jikinta, sai HINDU dake gefe tana rike da alkyabarta, domin sharadin NADIRAH sai dai idan da Innarta za'a je HINDU ta karra waigawa gabas da yamma, kudu da arewa, sai ta samu kanta da share hawaye tana karra wara idannuwanta tana kallo Tafkeken hotonsa dake makale, wanda rawaninsa mai shara shara ne ana gannin yannayin fuskarsa sosai ta zunawa ido, hakan ya saka ta ci tuntune da rigar Nadirar ta je ta gwarunma Nadirar Taga taga NADIRAH ta yi a dole ta kama Alkyabarta ta rike gam hankali tashe ta ce" annabi ka san da zuwanmu zamu rufto kasa!" Inna ta tareta raf tana fadin " Sannu Indi bamu kai kasam ba" Nadirah ta ja numfashi dan har ta rufe ido, sannan ta kama Alkyabar ta cire gaba daya tana jan numfashi ta kai dubanta wajen Umma zata yi magana Umma ta tareta da gagawa ta ce" Ya salam, Bahija sannu, baki ji ciwo ba?" Tsuru NADIRAH ta mata, sai kuma ta samu kanta da juyawa wajen da a shigowarsu take hangen kamar mutane Ido ta zuba masu itama, kamar yadda suka zuba mata, A hankali taa lumshe idannuwanta tana jin kanta na sara mata sanadiyar tino abinda ke boye Daga Auta kuwa, har HUZNAH idannuwansu tamkar zasu mana mata shi a jikinta hakane Fuskarta babu kwaliya ko diz a jiki, Dinkin dake jikinta doguwar riga ce ta leshi fari fal bashida ko digon wata kalar daya a jikinsa, haka kuma dinkin ya bi jikinta ya lafe a jikinta ya amshi jikinta har kirar jikinta Gashin kanta dama ba'a daura mata dan kwalin ba, alkyabar kawai ta rufa dan ita aka bari ta shirya ita kuma ta yi yadda ta ga ya dace da ita Kunnenta dan siririn dan kunne ne, hannayenta ba komai a jikinsu, sai sarkar dake kafarta a daure wace ana ganninta a bayane Mikewa suka yi dan karamata, da kuma yi mata sannu HUZNAH, jikinta har rawa rawa yake tana karra kallon NADIRAH, sai dai gannin kamar bata masu kallon wulalanci ba sai ta samu kanta da dan sauke ajiyar zuciya Auta kuwa ta rasa me take ji a ranta game da matar, ita dai ta zuba mata ido tana son karantarta Ba tafiyarsa ta sheda saukowarsa ba, domin takalman dake kafarsa na fata ne, basa kara idan ana tafiya da su Fankamemen madubin dake kafe ya sheda mutun zai sauko, hakan ya sa a tare suka juya kowa ya daga kansa dan gannin ko wanene Abin mamaki, kasancewar rabonsu da shi tunda safe dole zasu masa gaisuwa irin ta dukawa, ciki harda Umma domin wannan din hakan yake, Uwa uba HINDU da har neman kwonci take yi bama dukawar kasa gaba dayanta ba, ya zamto NADIRAH ce a tsaye, kanta a sama tana kallon saukowarsa cikin nutsuwa, da sandar dake hannunsa mai ruwan zeba tana walwalwal, da alkyabar dake jikinsa, uwa uba da rawaninsa mai masifar kyau wanda ya hau da shigarsa mai tsari da kyan gaske, a gangaro zuwa farin hannunsa kar mai jimke da sandar, dayan kuwa a cikin Alkyabar, haka kuma girman jikinsa wanda koda a cikin alkyabar ne ana iya ganewa da bashida karamin jiki, da irin nagartar shigarsa mai dukkan kirji A hankali ta yi luuuuuuuuuu da idannuwanta a lokacin da idannuwan nata suka shiga cikin nasa, sai kuma ta gane jikinta babu abinda ke nufi da itace BAHIJA watau Alkyaba Juyawa ta yi ta karasa kusa da Umma ta rage tsayinta kadan ta ce" Bani abin na rufa" Umma ta dago daga sada kanta ta mika mata alkyabar ita kuma ta gyarata kawai ta wani yafata a kafadunta sannan ta sake duban Umma da ta fara mikewa tana sake yi masa sannu da saukowa ta karasa kusa da NADIRAH cikin dabara ta shiga fitar da hular alkyabar ta dora mata a saman kanta a tausashe tana murmushi ta ce" BAHIJA, ki karasa ki gaisar da Mijinki mana" A hankali ya karra zubawa wace aka kira da BAHIJA ido, wannan karron ba duba daya da dauke ido ba, duba irin na tsanake dan ya gane me kennan?, Tun daga kanta har kaffafuwanta yake kallo sannan ya sake kallon Umma wace sam bata gane abinda ke wakana ba, burinta su daidaita dan ya yarda Bahijar ce a gabansa Umma ta rike hannun Nadirah suka karasa wajen zaman , gefen daya, ba inda su Auta suka zauna ba ta nuna mata tana fadin" Zauna a nan kema sai ki kawo gaisuwa" Zaunawar ta yi tana sake leka Innarta, ko dai inna ta summa? Take ayannawa a zuciyarta, Haka kuma a koye koyen abubuwan nasu sun manta basu koya mata baban abin ba, watau gaishe da UMUGHLUK ITIBEL, ai su basuma kawowa ransu cewa sai an koyar da ita wannan ba, gannin ita fa yar bayi ce ko? Bata sake kallon idannuwansa irin na dazu ba, bale har ta lura cewa kallon da yake mata ya gane ba ita bace Bahija a fuzge ta ce" Sannu da saukowa" Ba Umma da su Auta ba, harta Innarta sai da ta ji kamar an gaura mata mari , irin da busashen hannun nan, marin nan mai zafi da bada sautin DAU a kunci! A rikice Umma ta dubeta , sannan ta dubi ASADEEK da ya sake komawa da kyau saman babar kujerar da take tasa ya hade kansa da kujerar ya afka tunanin me hakan ke nufi? Ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 2️⃣9️⃣ A rikice Ummaa ta ce" Har yanzu bataa dawo normal ba, Bahija ko mu mayar da ke bangarenki ne?" Shiru ne ya dauki wajen, domun Itama NADIRAH sai ta samu kanta da yin shiru tana ta auna me ya dace ace ta ce? Baba ne ai ya daace ta duka ne ai tana gannin ta gaishe shi a duke haka Ajiyar zuciya ta sauke ta dauke kanta daga kan Innarta wace dama sai da aka ce mata idan sun zo a matsayin baiwa zata kasance har su koma Idannuwanta ta sake ɗorawa a kansa A facing dinta yake, domun kujerarsa na kallon su ne gaba daya Yawu ta hadiye aa hankali ta sauko kasa gaba dayanta kantga a kasa ta furta" Barka da warhaka, Fatan aan sauko lafiya?" Dama dama, watau gaisuwarta mafi dama da sauki kennan, mafi daraja kennan, sai dai kashhhh tun a nan ta tona kanta cewa ita din ba jinnin sarauta bace, domin ko Umma a yanzu ta wuce gaisuwar nan bale UMUGHLUK ITIBEL Ga mamakinta sai ta ji muryar mutanen da suka fi kusanci da shi sunna nema mata afuwa, bayan bata ga laifin da ta aikata na hakan ba Daya bayan daya ta shiga binsu da kallo, tun daga kan Ummar har wace keda fuska kamar ta yara sai shegen kallon tsiya Baki ta dan tabe ta nemi mikewa, Da sauri Umma ta mata alamun kar ta mike daga tsugunin nan, a dole ta sake gyara tsugunin nata tana girgiza kai irin abin nan fa ba zata iya ba walahi! A hankali ya dago kaansa dake jingine idannuwansa a lumshe y bude su y fara sauke dubansa a kan Umma, wace ke gurfane kanta a kasa Tambaya ce ke saman lebensa, wace take daf da fitowa daga bakinsa, itace wannan din kuma wacece? Sai kuma ya ji wani sashi na zuciyarsa na yi masa wata tambayar, shin UMMA bata san Bahijar bace aka miko mata wannan a matsayin Bahija? Wannan din wacece? Me yasa aka ce za'a bashi auren Bahija aka bashi na wata? A sanninsa bafansa y'arsa mace daya tak ce, itace wace suka yi tafiyar nan tare, bayanta a ina ya samo wannan?, Alamun wannan sun nuna ita din ba yar gidan sarauta bace, domin dan gidan sarauta ko yaro karami in dai ya fara iya hada magana ya iya gaisuwar sarki "Allah ya huci zuciyarka, yarinta ke dawainiya fa ita, a yafe mata, tana tuba in sha Allah ba zata kuma aikata makamancin wannan gangancin ba" Umma ta sake fadi a tausashe tana sake sada kanta "Yarinta?, Ganganci? Wannan din ai ya fi karfin ganganci ga mace ɗaya tilo da aka bashi a matsayin BAHIJA, lalle sunne suka yi ganganci wajen manta abu mafi mahimmanci, to shi a yanzu tamabayar da ta maye gurbin wacece wannan din itace....menene dalilin yin hakan? Ko yace menene mission din da aka ba wannan din?, Shi sai yake gannin kamar fitsarariya ce yarinyar, jama'a wannan kallonsa da take yi ido cikin ido fa?, Ga kuma gaisuwa irin sako da sako A hankali NADIRAH ta sake satar kallon Umma, to wai ita a ina du ta fadi magangannun nan da ake cewa ta ce?, Uhum, wai yarinta ganganci, zaki ga aikin ganganci kuwa A hankali ya gyada kansa yana sake dauke dubansa ya sake mayarwa kan Auta Ido hudu suka yi da Auta, sai yake karantar kamar ta afka a tunanin son gane yarinyar nan a cikin mahaukatan ita baba ce ko? A hankali ya sauke dubansa a fuskar HUZNAH Idannuwanta cike da lamari irin na rarashi da girmamawa, shigarta ta birge shi sosai, itama HUZNAH leshen ne yanaga a jikinta, kuma dinkinta sakake sosai , Huznah kam akoy hankali Kan matar dake duke, wace yake kyautata zaton baiwarta ce ya sauke dubansa, tun dazu take duke haka, sai ya samu kansa da yin gyaran murya yana duban matar Shirun da ya gani bata tashi daga gurfanawarta ba ya saka shi sake dora dubansa a kan Umma Lalle matar nanma ba ta gidan sarauta bace, ba kuma baiwa bace Da sauri Umma ta mike, kafafuwanta har sunna neman yi mata nauyi, rabonta da shiga dimuwa irin haka tun wani lokaci da mahaifiyarsu ta tardota tana zane Auta, A hankali ta dafa Inna kasa kasa ta ce" yana nufin kina iya tashi" Inna ta dago tana jan hanci ta saci kallon y'arta, oh duniya yau ga abin jibga Indi ta yi ba halin ta zauneta ta jibgeta? Innalilahi ita HINDU ashe zata ga wannan rana irin haka? Dole yau ta Jibgi Indi walahi! Kanta a kasa ta shiga kokarin kamanta gaisuwa da neman afuwa kamar yadda ta ji matarsa da kanwarsa da Umma na yi, sai dai itama bata san a yi masa maganama masu wannan yancin kai tsaye makusantansa ne A hankali ya jimke hannunsa jin kamar bacin rai na neman hadasa masa mijirya a gaban jikinsa Umma ta salami HINDU fuskarta har tana gyatsine dan rikicewa A hankali ya budi bakinsa maganar farko ya ce" Umma, kina iya tafia" Umma ta kalle shi, hankalinta a tashe ainun, sai dai ba damar jan maganar dan an masa laifuka a jejere sosai A hankali ta karra neman afuwarsa sannan ta nemi da NADIRAH ta mike su tafi Da mamaki Auta ta kalleta, hakama HUZNAH HUZNAH ce ta yi karfin halin fadin" Aa umma ki je zata zo, bamu gaisa ba fa" Umma ji ta yi kamar ta karasa ta shaki wuyan HUZNAH ta gaura mata tagwayen mari, sai dai ba hali, a hankali ta saki.lalausan murmushi sannan ta kafe NADIRAH da ido, wace ke duke ba'a bata damar tashi ba, ita gaba daya bama fahimtar wannan magama kamar masu ciwon baki take yi ba, kamar ta yi kisa ? Wai shi sarkin adalci? Walahu harda zalunci a jerin sunnayen nasa , in ba wannan ba me ta masa daga haduwa? Koda yake mutumen da ya tsofi su Inna ai sai hakuri da hali, itafa kowama ya kama kansa fa, itafa bata zo wajen nan dan komai ba sai dan ceto, ceton kuwa zata yi shi ne ta hanya daya tak, idan sun tashi karshi ta fada masa, dan ba zata iya kayan takaici ba,wani zuwa gaishe gaishe da sauransu gaskiya bata so, ita da ta so ta fita bayan magaribar yau ta zazaga masarautar babu alkyaba? Ta gaji da zaman dakin ya fara hadasa mata ciwo Jiki ba karfi Umma ta juya ta fice, ji take dama tana iya zama kuda ta lane a jikin NADIRAH ta ringa daidaitata?, Ya Allah! Tana fita Auta ta sake kallon Yayanta A sanyaye ta ce" Abah, ta mike daga tsugunnin? Ta tuba a gafarceta" Baki NADIRAH ta turo kai kace zaa saka mata ribom ne a daure ta kalli Auta da kallo irin na harare harare wanda hakan ya saka Auta zarro ido tana kallonta Bai ce komai ba ya mike a hankali ya juya ya shiga haurawa sama, wanda hakan ya saka Matarsa mikewa da dan sauri ta bi bayanshi NADIRAH dai da ta dafe kugu sannan ta kai zaune a fili ta furta" A gayasssss" wanda sam bata san ya fito fili ba Auta ta sake wangale baki da zarro idannuwa kamar zata fado dan mamaki tana kai hannunta daidai bakinta ta furta " Lah " NADIRAH ta dago tana kallonta, samun kanta ta yi da karra kallonta itama , sai kuma ta ce" Yo tsakaninki da Allah me na masa ni, tun dazu kuke cewa na tuba kuma bakwa fadin laifina, shikenan dan nice bakuwa sai a cuceni? Haba dai" Da mahaukacin mamaki hadi da wani zarro idon Auta ta ce" Aban ne zai cucekin ko wa?" NADIRAH ta yi shiru tana kallonta, sai kuma ta mike tana kabe Alkybarta kamar ta yi kasa din nan ta ce" Babanki ne kennan?" Auta ta girgiza kai tana murmushi itama ta mike tsayen tana kallonta ta ce" Yayana ne" NADIRAH ta kama haba da mamaki ta ce" To fah, shi kowa Aba yake ce masa ne?" Auta ta dage kafadu tana jin mamakin yadda Bahija ke magana a sake, irin ba abinda ya shafetan nan NADIRAH ta ce" To sai an jimanku, bara na koma na san ana cen ana jirana" Auta ta yi saurin fadin" Da wuri haka zaki koma? Ga fa abincin da aka tara mana saman table" NADIRAH ta waiga wajen abincin, tsarin kwanonin kadai abin birgewa ne, sai dai a ranta ta ayana' kai ina, aje an zuba gubar a ciki' a bayane kuwa sai ta ce" Aa a koshe nake fam da kika gani a nan, a ringa bismillah dai in za'a ci abinci...... .." Daga haka ta yi ficewarta hankali kwonce, ta bar Auta cikin tatauna maganarta Haka kawai sai Auta ta ji kamar da wata manufa tace a ringa yin bismillah Sai kuma ta koma ta zauna tana murmushi, rabonta da ta ga rikicewar Umma haka an jima walahi, Ama wannan matar ko wacece ta birgeta, sai ta ji kamar kar ta tafi , kamar ta yi ta zama da su a nan din, tunda ta shigo wajen ake haba haba gwanin dadi A tsaye take a gefensa, bayan dogon hakurin da ta bashi har ta rufe bakinta bai bata amsa ba Sai da ya gama yanke shawarar abinda zai yi ya dubeta yana murmushi ya ce" Ba komai fs, ki je ku ci abinci" Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta juya ta tafi Wayarsa ya dauko yar karamar ya zauna a bakin bed yana warware nadin Rawanin dake kansa A hankali ya shiga wajen tarin uban miscall din da yake samu na number da aka duba masa aka tabatar ko ta wacece Number ya dauka ya turawa yaronsa sannan ya rubuta masa mesage cewar a yi gagawar yi masa tracen number nan zai yi kira a sanar masa ina mai number take? A nutse ya gyara zamansa sannan ya danna kiran ya ajiye wayar a kusa da shi yana dan shafa gemunsa idannuwansa sun kada sun cenza launi Wayar na fara kuka aka daga, ringin ko na biyu bata yi ba aka daga hafi da sauke wata nanauyar ajiyar zuciya murya a birkice da kukan dadin gannin kiransa ta ce" Asalamu alaikum yah habibih" ASADEEK ya sake murza sajen habarsa cike da takaici a takaice ya amsa salamar da lalausar muryarsa da karyewar harshensa tamkar balarabe BAHIJA ta kai zaune tana kashe TVn dake kida ta dora hannunta daidai zuciyarta ta ce" Ina ka shige? Dan Allah ina ka shige? Har na cire rai, na yi kukan har na hakura, kulun cikin tunaninka nake, ka bani number na kira na kira ba amsa, tun bata shiga ta zo tana shiga, mamana tace ta yiwu aiyuka sun maka yawa, dan Allah ka fada min a wani gari kake a NIGAR zan zo, idanma baka da lokaci ni zan zo" 'innalilahi wa inna ilaihi rajune, ya Allah ya Allah me yake faruwa da ni ne? Wace aka daura min?...........' A kala ta dauki minti daya tana ratabo zance na rashin kamun kai, har ya tabata ko menene sun gama masa a sanyaye ya furta" Zan yi kiran ki, zan je na dawo" Muryarta a sanyaye ainun ta ringa magiyar dan Allah kar ya manta ya yi kiranta dan Allah tanada wata mmagana mai mahimmanci da zata sanar masa Uhum kawai yace ya katse kiran, A nutse ya mike ya shiga cire kayansa dan ya fara jin sun masa nauyi Ya rage daga shi sai karamar rigar ciki da wandon shadar da ya cire Kiran yaron nasa ya shigo, nan yale sheda masa daga garin Tanut ne, harta da anguwar sai da ya sanar masa Wayar ya tsurawa ido, still kirjinsa na dukan tara tara A hankali ya lalubi number SHEIK Wayar na fara ringin shima ya daga a kamilance ya yi masa salama da gaisar da shi ASADEEK ya bude idannuwansa yana fadin" Da wa ka daura min aure ne Sheikh?" Sheikh ya yi shiru dan bai fahimci hausar ba, sai kuma ya dan gyara zamansa ya ce" Da yar gidan Sarkin Tanut ko? NADIRAH wace ake yiwa kiranye da BAHIJA?" Wara manyan idannuwansa ya yi, da karfi ya damki abin rufar gadonsa ya jimke yana rintse idannuwansa, hakan ya sa jijiyoyin jikinsa mikewa birde birde Muryarsa a cinkushe ya ce" Karfe bakwai ina son ganninka a sashena in sha Allah" Daga haka ya kashe wayar ya sake gyara tsayuwarsa yana ta aunawa, abinda yake ta korewa baya son kawowa ransa shine, Umma ce ja gabar auren nan fa, me hakan yake nufi? Umma ce fa? ...........( Uhum )................. NADIRAH hankali kwonce ta bude bangarenta, watau baban kofarta ta shiga, domin ta hanya sak ta biyo tana salama a saman lebenta Mikewar Umma kawai suka gani, sai saukar yan yatsunta biyar a saman kuncin NADIRAH, wanda hakan ya kusan gigitata, domin wani ihu ta saka wanda ya saka innarta zaburowa hankali tashe ta nufo wajen tana kama sunnan Nadirar da karfi Umma ta nuno su gaba dayansu ranta bace ta ce" Wannan shirmen, da gidadancin, da kauyancin da kika yi yana daf da tashin hankalinki, da cire numfashinki, daga ke har iyayenki, domin ni nan da kika ganni ba zan taba daukan wahalarku ba walahi!, Me yake damun kwakwaluwarki? Ko mahaifinki ne kya masa wannan gaisuwar bale wanda ya fi shi daraja?, Ina ce an ce maki idan baki san abin fada ba ki yi shiru?, ASADEEK zaki duba ki ce masa barka da saukowa?, Yana saman kujera kina bakuwarsa zaki haye darr ko zauna?, Yana cikin fushi kike kallon idannuwansa?, Karya kike yar talakawa yar bayi! Karya kike idanma kina nufin ke baki iya bane!, Mu zaki kawowa shirme? Mu zaki kawowa maganar banza?, Idan har gangancinki ya haifar da rashin yarda sai dai ke ki kwana ciki, yanzu ki fada min bayan fitata me kika karra aikatawa na hauka?" NADIRAH da ta fashe da kuka a jikin innarta, innarta ta dagota murya a shake ta ce" Ki kama min baki, ki min shiru, marin na waye baki sani ba?, Ki min shiru nace!" Kukan nata ta ringa shanyewa, idannuwanta jajari ta kai dubanta kan Umma Zata yi magana Innarta ta tareta tana rufe mata baki Innarta ta dauke Umma ta yarfa da asakaran kallon da ya saka Umma zuba mata ido Rai Bace HINDU ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣0️⃣ Rai bace Hindu ta ce" Mari? A fuska? Waje mai daraja? A kan laifin da ba'a koya mata laifi bane? Ita fa bata rayu cikin gida irin naku ba, a sake ta rayu fa, hakan bata san laifi bane ba fa!" Umma ta sake zubawa yannayin Hindu ido, tabas ta karanci ranta a mugun bace yake, a yannayin da take magana tana dan bari zai tabatar maka tana hanna kanta wani abu mai girma ne Umma ta sake kallonsu su dukansu sama da kasa, sai kuma ta juya ta fice ba tare da ta karra furta komai ba HINDU ta juyo kan Nadirah, stilll ranta bace ta mata nuni da dakinta a kausashe ta ce" ki je ciki" Nadirah ta juya jiki amace tana jin kamar fuskarta ta sundume ta shige dakin nata HINDU ta tafi ta rufe falon ta dawo ranta a bugun bace ta ringa doka hannunta a kasa tana cije lebenta har sai da ta samu hawayen sannan ta hade kanta da gwuiwarta tana shashekar kuka Wannan shine daidaikun kalubalen da y'arta ke iya fuskanta Rayuwar rashin yanci Wannan shine abinda ke iya zuwarwa Nadirah a ba zata , domin a tunaninta haka din abu ne marar tsauri, ba wani laifi ta aikata ba a tunaninta, idan har aka yi duba da wajen da ta tashi, za'a iya yi mata uzuri Gannin ta kasa daina kukan zuciyarta na daci ya sakata shigewa ciki ta dannawa yayarta kira Rai bace take labartawa Fadime abinda ya faru har zuwa marin FADIME ta lumshe idannuwanta a sanyaye ta ce" HINDU, tsaya ki ji, a irin hukuncin da ya dace yarki mari an mata mai sauki, sannan kar ki ji wai, idan har ta yi sake ya gane tabas zai fito neman ba'asi da karin haske, domin abinda ta yi ba aiki bane na ƴaƴan sarauta" HINDU ta ce" Aunty, ama kina tune, abinda aka koya mata an koya mata gaisuwa? Ko ta yi zaman da zata ga yadda kike yi? Ba ita ba, nima fa ban iya ba" Fadime ta ce" Haka ne, ama abinda nake so da ku baki daya shine, yanzu ya dace ku zauna ku karanci damuwarku, ku samawa kanku mafita, kar ku ringa manta abinda ya sakamu shiga bakin kura mana, ya dace ta aro halayan yayan sarakan koda bata sansu ba, ya dace a yanzu ta koyi kamantawa, in sha Allah da safe zan mata dogon kwatance na gaisuwarsa, dole ne ta bi dan gudun tonuwar asorinmu baki daya kin ji Innarta?" HINDU ta gyada kai bata ce komai ba Fadime ta ce" Ki daina kukan haka, ke da zaki karfafeta, Mari ai da sauki a kan abinda take iya samu matsayin hukunci, ta yi garaje Innarta, ba'a haka, ai Allah ne ya nada sarki kuma yace a yi masa biyaya ko?" HINDU ta gyada kai, a hankali ta ce" Kuma Allah ne ya halata wasa tsakanin miji da mata, ya halata sakewa da hira tsakanin miji da mata, wace ta zarce tsakanin kowa, bai bambance cewa matan sarakai kar su yi irin haka a tsakaninsu ba ko?" "HINDU, kar ki manta tsakanin da abinda ke boye, " Fadime ta fada Hindu ta ce" Shinema abinda ya fi sakani gannin idan yata ta kula alaka ta sabo da shi, zai zo mana da sauki, ina gannin a yadda ake zuzuta daukan mataki a kan laifi a wajensa ta fito da gala mai girma tunda bai dauka a kanta ba, Aunty sabo yana da dadi" FADIME ta ce" Haka ne, ama ta iya takun rawarta, kar ta bata ta da tsale, ta iya kame bakinta kar a yi mata kallon wace tale da sakin kai da halaya irin na yan gajaliya, ta kasamce mai taushi dan mace take, uwa uba kar tace zata takaita tafiyar dan zuwa ta yi ta koma, babu abinda ya gagari yarki, kin sani sarai, idan har ta saka gagawa ko raini a ciki, zata sa a gane da wuri a daura mata laifin komai da komai, bayan ita laifinta daya ne tak a tafiyar nan, yiwa iyayenta biyaya" A sanyaye HINDU ta amsata, suka ci gaba fa zantawa, a yau din Fadime din da kanta tace lalle tana so HINDU ta fan karra zama kadan, ba dan komai na, sai dan ta wanke kanta, abinda NADIRAH zata fara da shi dan wanke kanta shine aikawa da sakon zata ziyarci kishiyarta, daga nan idan sun je ta nemi alfarmar ta mata rakiya ta ba UMUGHLUK ITIBEL hakuri domin rashin lafiya ta dakata yin wasu abubuwa mararsa dadi, harta abinda ya dace ta fadi a gaban UMUGHLUK ITIBEL FADIME tana ta sanarwa HINDU, har dai ta dan fahimci wasu abubuwan sannan suka yi salama ____________________________________ Washe gari daga masalaci yana dawowa ya shige ciki ya kimtsa sannan ya sauko dan ganawa da SHEIK Umarni ya bada kan kar wanda ya shigo, yana da bako Sheikh dai kallonsa yake yi, dan ya fuskanci ko barcin kirki bai samu ba A nutse ya dubi SHEIK ya ce" Yarinyar da suka aura min, ba wace na sani bace" A nutse Sheik ya dake fuskantarsa, a hankali ya ce" Bam fahimta ba, Allah ya taimakeka" "Ina nufin wace aka ce da kai itace Bahija, ba ita bace" ya bashi amsa yana dan hade hannayensa Sheikh ya dake dubansa da mamaki ya ce"Ban fa fahimci yarenka ba, Allah ya karra maka lafiya" ASADEEK ya ce" Abinda kake ji shi nake nufi, ita yarinyar ta wajensu mun yi tafiya da ita Haji, na ganta, na kuma santa,wace na gani jiya ba ita bace" Gaban Sheik sai da ya fadi dan abin wani iri ya ji, ya gyara zamansa shima da kyau ya ce" Wannan wace irin magana ce, gaba daya na kasa gane inda ta dosa, ba ita bace? Wacece? Me hakan yake nufi? Yaya aka yi ka iya ganewa cewa ba ita bace kai da baka yiwa mutun kallon tsaf?, Mahaifinta fa ya jadada min cewa ita ce, sunnanta na kirki ne NADIRAH, ama ana mata kiranye da Bahija a lokacin da na tambayeshi dama Bahija sunnanta NADIRAH? Duba da ka sanar min sunnan yarinyar" Komawa ya yi ya zauna da kyau yana lumshe idannuwansa, ya jima a haka sannan yaa sake budar bakinsa a nutse ya ce" Idanma wacece wamcen, wata ce daban, wace ba Bahijar ba, domin bahijar a yanzu haka tana Tanut, wannan kuwa zan iya ce maka kamar ba yar cikin gida bama, dan ta fi kama da yar fashi!" A zaburw Sheikh ya sake dubansa da yannayi na mugun mamakin sunnan da ya hada yarinyar da ita Bakinsa har yana hadewa ya ce" Subahanalah yar fashi kuma?" ASADEEK ya gyada kansa, sannan ya nunawa SHEIK wajen kujerar da yake zaune ya ce" Ka ga a nan, a nan ta kalleni shekeke tace min sannu da saukowa,wai sannu da saukowa, ko daga ina? Kamar ta sha kwaya a lokacin dan na kula tana ta layi, sai da aka rufa mata alkyaba fa, kowa na duke yarinyar tsayina da nata a laye, inaga in ba yar fashi ba to bata da hankali" Sheikh bai san lokacin da ya ringa juya kai yana ambaton Allah da mugun mamaki ba, toh fa, gaskiya ne akoy matsala a tare da yarinyar, yo ko ba yar sarauta bace ai mugun mugun girmansa na sakawa a duka gaishe shi fa, kuma gaisuwar ce kanta sai a hankali gaskiya, oh ya godewa Allah da baya nan😔 Sai kuma ya samu kansa da damuwa da tunanin ama me ya sa Bafan ASADEEK zai aikata haka? Da yannayin damuwar ya fitar da tambayar ASADEEK ya dube shi ya ce"Ni bama wannan ba, Bafa ina iya ajiye haka a wani bigiri daban, tambayar da nake son yi yanzu shine Umma, shin UMMA bata san Bahijar bane kafin auren ko menene?, Na ga ita ta amso yarinyar ita kuma ta ci gaba da gabatar da ita matsayin Bahija, ina so a kirawota yanzu dan kaina ya fita daga duhu" A hankali SHEIK ya fuskanceshi, a sanyaye ya ce" Ni kuwa da zaka amince da na kawo wata shawarar Allah ya karra maka lafiya" Dubansa ASADEEK yake yi, har ya yi niya dan kansa ya furta" Ina sauraro" SHEIK ya sauke ajiyar zuciya , cike da yannayi na son convincing dinsa ya ce" a lamarin nan ina hangen wata sarkakiya, wace da son samu na yi, mu bita a hankali, sannan mu hadata da ayar Allah, Allah ya taimakeka na tabata ko a yanzu da muka dan fahimci wani abin, ina nufin wanu abin ya fito fili Allah ne ya haska mana, ba isanmu, da dabararmu ba......, " UMUGHLUK ITIBEL ya sake dubansa, a nutse yana fitar da harufan a daidaice ya ce" Kana nufin, na yi shiru ko Umma kar na fadawa maganar nan?, Kana nufin na yi shiru a gaban yarinyar nan karama kamar mai shigar aljannu ina kallonta a matsayin wace ba ita ba?, Kennan ni abinda nake jirab sani da wancen din fa ya fadi a banza? Sai na salameta ta tafi tunda babu amfani dama wannan ne anfaninta" Ido Sheikh ya tsura masa, duba yake yi masa irin na dama na san da wata manufar ka aminta da maganar auren nan, Fuska ya hade sosai yana dauke kansa, irin baya so a sake dauko maganar kwata kwata, domin ba irin tsarewar da Cheik bai yi masa ba a kan maganar ya nuna masa ba wani abu a kasa aure aka bashi ya amsa, CHEIK ya gyada kai yana sauke ajiyar zuciya a hankali ya ce" Ko me yake boye a cikin lamarin nan kamar yadda nace ne, ba rikicinmu zai bamu ba, sannan ka sani a yanzu ina so ka rufe mata wannan magana, ko me take kunshe da shi ka kyaleta, kuma wannan yarinya da daya rana kar ka nuna mata ka san komai, hasalima ka jata a jikinka ko zamu fahimci abinda yake boye, kar ka manta Allah na fitar da fari a cikin baki, yakan kuma fitar da baki a cikin fari, Allah ya karra maka lafiya da nisan kwana bamu san me hakan yake nufi ba, ama zamu bashi damar bayanar mana da kansa in sha Allah " Numfashi ya sauke , ya mayar da kansa ya jinginar, A hankali ya furta" Zan yi tunani a kai" CHEIK ya amsa da "Allah ya baka ikon yarda da abinda na ce" Shi dai daga nan bai ce masa komai ba, girmama girman rainin yake yi a zuciyarsa, kuma yana tunanin anya zai iya boyewa Umma kuwa? Idan ya boye mata anya ba zai hadasa masa wata matsala ta rashin yarda da ita ba kuwa? Abin ya tsaye masa a zuciya ainun, har CHEIK ya yi masa salama ya tafi yana fadin sai ya fito Fada in sha Allah _________________________________ Yadda Umma ta ga dare, haka ta ga rana Wayar da ta kwana bugawa tun jiya sai yau aka daga Bata tsaya wata wata ba ta ce" Kina tunanin yarinyar nan da wace ta rakota sunna iya hadasa min da matsala a kan abinda nake gannin mun kawo ga ci?" Gimbiya ta yi siririn tsaki, da wata masifar ta kwana, BAHIJA ta rikice wai sun yi waya da balarabenta ama yace zai kira shiru har safiya bai kira ba, sai kuka take yi gana ta kira ya ki dagawa, ita kam wannan masifa ta balarabe anya ba zuwa zata yi a nemo mata inda zata ganowa y'arta shi ba?, Wannan abu ya fara daga mata hankali sai ga wani shirmen kuma A dake ta ce" Ban fahimci yarenki ba" Umma ta sanar mata dukkan abinda ya faru, daga farko har marin nan na jiya Da takaici Gimbiya ta ce" Wannan wani irin sake ne? Ita wace ta rakatan me take yi har yanzu a cen? A kan me zaki bari har haka ya ringa faruwa ? Ina fata ba wani tunani gareki a kan yarinyar nan ba ko?, Dan kina iya janyowa kanki wani abin, kuma ki sani idan har muka yi sake mune a ciki, dan haka zan tado mutun ya kawo maganin nan, zan amsa daga wajen Aban Bahija a kawo a saka masa ya ci kowama ya huta!, Ita din bamza yar talakawa zamu yarda ta kawo mana cikas din ne? Bata isa ba, uwartama bata isa ba bale ita, ke kuma idan haukanki ya saka ki aikata aiki irin na sake ai shikenan!" Da wutar ciki itama ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣1️⃣ *Asalamu alaikum jama'ata yan uwana masoya yan albarka grup SAJIDA PALACE, ina matukar godiya, ina miko maku fa godiyata, ban amsa maku tarin comment bane dan ban zauna ba, ama zan amsa ku kun san son so ne fisabililah💓💓💓, my zuciya na yin bubuduk idan ina karantaku😂, kaunarku da kaunata sun riga sun makaleni a kuluna, shi yasa zan wankeku da biyu matab albarka* Da wutar ciki itama ta ce" Aikin da kuke fadin zan aikata kina wani karra maimaitawa ai ni ban taba boyewa ba, gwara ni da ke, kema kin san abinda nake nufi, kuma da kike fadin idan sun isa su gwada tambayarki na yi, ki tabatar min domin dan na mareta Matar nan ta min wani kallo da rabona da na ga irinsa tun a lokacin da na rungumi kanwar Asadeek da tana kukan mutuwar iyayenta, idan kun san wata jaraba kuka hadoni da ita sai ku sanar min na dauki mataki, dan ni babu wanda ya fi karfina!" Tsaki Gimbiya ta ja ta kashe kiran ta wurgar a bayyane ta ce" Shashasha ko ita wa? Idan ta tashi burgarta ta rufe ido ta ringa ihun babu wanda ya isa ya fi karfinta, zaki ga fin karfi ne, domin wannan aiki da za'a aikata tsumi tsumu sai kin samu kanki a ciki, sai na ga ta tsiya, karamar aniya!" Tana maganar ne tana rufa alkyabarta bata tsaya kula kowa ba ta dauki hanyar bangaren mijinta, dan ta tabata da wahala in ya yi sallar asubahima , ta yiwu yana cen yana rizgar barcin asara Tana zuwa ta kwashi wani kayan haushin Sama sama ta ringa jiyo muryarsa yana fadin" Yauwa yar albarka rike da kyau, dan matsa kan kin ji?" Zama ta yi tana ta karkada kafa a falon har wani yangwamamen ihunsa ya karade wajen sannan ta ji shiru Mikewa ta yi ta shige dan ta tabata a irin lokacin shi kuma ya shige bayi dan ya wanke jikinsa Tana shiga ta bi yarinyar da kallo, yarinya karama, sam bata santa a masarautar bama bata taba ganninta ba A rikice yarinyar dake goge jikinta da ya bata mata da wani ruwan jikinsa mai gari gari ta shiga rarumar kayanta jikinta na rawa tana kallon gimbiya da neman fashewa da kuka Bata ce mata komai ba sai da ta gama saka kayan nata sannan ta karasa ta mata wani shaka wanda sai da ya saka yarinyar fitar da idannuwanta waje a rikice tana kallonta A kausashe Gimbiya ta ce" Kin san hukuncin fitar da maganar kin zo dakin nan kin aikata wani abin ko baki sani ba?" A rikice takebada amsr ta sani muryarta na fita da kyar Gimbiya ta saketa ta karasa ta buda kayan mijinta ta dauko kudi ta watso mata sannan ta amshe wayarta ta cire layukanta ta nuna mata hanyar fita A gurguje ta idasa daura nikaf dinta ta fice hankalinta tashe, du gani take yi kamar biyota zata yi ta kasheta, domin a cikin gari sunnanta ya baci iya bacewa Fitowa ya yi yana dan washe baki dan ya gama zubar da tsiyarsa a titi Turus ya yi gannin Gimbiya, sai kuma ya daure fuska yana fadin" Meye?" Gimbiya ta kwashe shi ta watsar tana cire kanta ta ce" Jakadiyar Kasar AGADAZ ta yi kira a kan abinda ya fara fuskantarta, shine nace za'a turo da maganin nan a yi abinda ya dace tunda wuri, dan bana son lamarin wasa, tunda farko na so ace an yi, idan gangancinta ya saka ta aikata abinda za'a gane ta sakamu a matsala kennan" Dakin ya karra bi da kallo, ya kalleta kamar bai san me tace ba ya ce" Ke ima yar mutane?" Goshinta ta dafe da takaici ta ce" Ka san dai da ranshi ba zan yi wasan kashe yar mutane ba ko?, Ta tafiyarta " Kafadu ya dage ya kai zaune yana lalubo wayarsa ya ce" Na sani, abin naki ne wani lokacin kamar baki da imani" Da takaici ya kumeta kasa ce masa ci kanka ta yi, kawai ta yi zurru tana kallonsa har ya gama rage girman idannuwan nasa da kyar ya lalubo number Umma ya buga mata kira Takaici ya saka gimbiya girgiza kai, watu bama zai yarda da maganarta ba sai ya ji ta wancen ko? Bata tashi kallonsa a zabure ba sai da ta ji ya ce" To ke uban wa ya aike ki marin yar Fadimata?, Ku walahi kun cika neman jaraba, su fa basa dukkan ƴaƴansu, a laluma ya dace ku bita ba da masifa ba, sam baku iya cin ribar duniya ba kunna abu kamar mahaukata, ke baki tambayeta ta gwada maki gaisuwar ba kika dauketa firkyau firkyau kuka tafi?, Tunda kuka kwana ku dukanku har yanzu bai neme ku ba lafiyar ce, ki tashi kawai ki je yadda kika saba kicin da sauransu tunda kece da ikon komai matarsa hoto ce tana labe!, Zan gani zuwa jibi za'a kawo maganin sai ta gani in ta daidaita lokacin ta ga ya dace kawai ta bada masa, ke ko shaka masa ne ta yi a wuce wajen" A haka suka yi salama, gombiya na yi masa wani irin mugun kallon da ya sakashi rafka tagumi ya ce" Wani lokacin sai na ga kinai min kallon nan kamar zaki kasheni ki huta walahi" A ranta ta ayyana ' Dama inada wannan damar, da ina mai tabatar maka ba zaka kara minti daya ba' A bayane kuma ta ce" Kai kake bani mamaki, ina tsoron idan Allah ya tashi kamaka ka tube zirr ka bi Fadime da gudu, Allah shi kyauta" tana gama fada ta juya ta kama hanyar ficewa, shi kuma ya daga murya yana fadin" Ba amen ba bilahilazi, yar bakin ciki ni da ita ai yar daka ce ba yar hanya ba, sai dai ki mutu!" ( Wannan shine huldarsu, fahimtarsu, cin kansu, Allah ka sa mu dace) _____________________________________ Da yamacin ranar ta samu iso zuwa bangaren HUZNAH, ziyarar da UMMA bata ji ba kwata kwata, sai bayan isarta labari ya je mata daga bakin masu kai mata tsegumi, watau daidaikun mabiya bayanta Tarba ce ta salu ta gani ta fada, tarbar da ta bata mamaki, haka ta zuba ido tana bin yadfa suke gabatar da huldarsu zuciyarta cike da mamakinsu baki dayansu Bayan sun gaisa, su biyu ne a saman kujerun, sai bayin dake duke a kasa kowace kanta a kas , ba'a basu damar fita ba, dole zasu zauna ko me zai faru ya faru a gaban idannuwansu da kuma kunnayensu NADIRAH dake zaune, tauna kalmar da aka ce ta zo ta bada ta hakuri da abinda ya faru jiya take yi a harshenta, sai dai sam ta rasa ta yaya zata fara, domin a aunawarta bata ga menene girman laifinta ba, hasalima bambancinta da su shine bayar da hakuri a lokacin da ba'a aikata laifin komai ba Bayin nan kwaya hudu take kallo, kalmar dake saman harshenta ta samu fitowa a hankali ta furta" Ku bamu waje " Sai dai bayin da aka ce nata ne kadai ta ga sun mike sun fice bayan sun yi mata fatan a yi hira lafiya A nutse ta dora shemamun idannuwanta saman biyun da suka rage, wa'inda daya ce hasalin baiwar HUZNAR, dayar sunnanta dai ne baiwarta ama dukkan motsinta tana kaishi ne gaban UMMA Kallon da take yi masu, da hanna kanta dura masu ashariya gannin jam'u ta yi furucinta ama biyu basu basu wajen ba ya sakata muimui da baki tana karra kausasa dubanta a kansu Da yan yatsunta, ta masu alamun su fice, wanda hakan ya ba NADIRAH mamaki ainun, watau an nuna mata ga yadda ake sarautar ko? Sai dai kashhh, bata san ko a tsuman ranta ba domin ba wannan ne a gabanta ba Sunna fita ta dago dubanta ta dora saman Huznah Matar dai ta girmwga gaskiya, dan a yadda ta kiyasta zata kai shekaru talatin haka, ko da doriya, ama gatan wata zullu abinta ba'a cewa komai Akoy fa kyau dan kyau sai baranci....ta ayana a zuciyarta Kai tsaye, ta ce" Me yasa, a matsayinki na wace ta isa ta saka, ko ta hanna, kike zaune bakya shiga kicin ki girkawa mijinki abinci, ko baki iya ba?" Da sauri HUZNAH ta dago da idannuwanta, duba ta sauke a fuskar NADIRAH, wace take yiwa kallon BAHIJA, Sai ta ji kamar zaginta yarinyar ke son yi, ko tana so ta nuna mata cewa ita bakuwar jiya tsal har ta kai wajen da zata iya nuna mata son mijinta? Ko tana so ta nuna mata bata iya girki bane?, Sai ta samu kanta da tsare NADIRAH da ido, sakon da aka kawo mata an ce mata ne zata zo gaisheta, da bayar da hakuri, ama a zuwanta ko gaisuwar ce mata ta yi sannu fa da hutawa tanai mata wani kallo kamar ka tile kayan wankin nan, a tunaninta ko dan girmarta da ta yi ai ya dace ta girmamata ko?, Ko dan da ake cewa kishiya kishiya ce zata yi kishi da ita?, Ko nuna mata zata yi kusa ta fi kusa ne?, Ko kuwa tana so ta nuna mata ita yar sarauta ce?, To ai itama yar sarautar ce, idan bata da labari bara ta sanar mata A nutsenta ta ce" Mahaifina, shima sarautar ba cira ya yi ba ALLAH ya dattar da ke da tsufa a bisa girman darajarki BAHIJA" NADIRAH ta dan yi tsuru, gaba daya bata gane ina ta dosa ba, to ana zancen girki me ya kawo maganar mahaifi? Allah ta tuba itama nata uban ai sarkin ne, na dogarai,kowani sarki kuwa ai sarki ne a fadarsa wa bilahilazi! Baki ta tabe, ta ari yaren nutsuwar, domin ta kula idan ba halayar da Allah baya so ka dan aro ba ba zasu fahimceka ba, watau girman kai, ta yafa , a nutse ta ce" Allah ya huci zuciyarki....." Ta ajiye zancen tana tabe baki da tunanin me aka yiwa zuciyartama? Ta sake fuskantarta ta ce" Ban zo gidanki, fadarki, duniyarki, balbalin mijinki, dan na koya maki tafiyar da dukkan abinda ya dace ace naki ne......., Ki gane ban kuma fada dan na hadasa husuma bane... .., kawai gani na yi shi sarki mijin sarauniya ne, ba mijin makaraban gidan sarauta ba" Ta ajiye maganar tana wana manyan idannuwanta zuwa tsarin falon mai masifar kyau da daukan hankali A hankali ta mike tsaye , sannan ta dakata ta juyo tana kallonta ta ce" komin jimawar zaki a dawa, cikin kogo a boye, ba zai hanna kuraye wadaka da kai kawo ba, idan har ba giga ya yi ba, sunnansa na loko , fili kuwa na kuraye ne, Yin girki ba laifi bane a tunanina, idan har ba iya sarafa abin bane ya zamto gagarare a gareki Allah ya karra maki lafiya" Daga haka ta sakar mata malalacin murmushi sannan ta juya ta fice daga falon A rikice HUZNAH ta mike tsaye tana kallon hanyar da NADIRAH ta bi *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣2️⃣ A rikice HUZNAH ta mike tana bin hanyar da NADIRAH ta bi ta fita da ido Daidai nan Bayinta suka dawo, ita kuma a lokacin ta shiga kai kawo tana kai yar yatsarta karama ta dantse a bakinta cike da jin radadi da rukuki a zuciyarta A ranta ta shiga ayana magana kamar haka' Kin zo gidan nan ne da nufin takani?, A tunaninki sangartaciyar inna nake wace ke ci ta bar kwano a nan yashe?, Lalle ba zan yarda ki zo gidana ki sameni da mijina ba ki fara kawo min tsare tsare, ni nan ni zan fara yiwa mijina girki kuma zaki samu gayata a yau ba sai gobe ba!' Fuska a hade ta bada umarnin ko me ake yi a je a sanar a baban kicin na bangaren mai martaba zata shigo kicin da kanta A zabure yar rahoton Umma ta dubeta, sai kuma ta sada, a tausashe ta ce" Allah ya taimaki uwar bayin Allah, me ya hada ki da girki? Fatarki ai ba ta shiga kicin bace, sannan Allah ya karra maki lafiya kin manta Maman Ja gaba ce keda wannan alhakin?" Samun kanta ta yi da tsare matar da kallo, idan har tana iya irgawa a gidan nan ai komaima maman Ja gaban ce keda alhakinsa, ciki harda hurumin da ya dace ace nata ne ita matarsa, ya dace ace Umma tana kula ne da abinda ya shafi abincin bayi, ta bar mata na mijinta ita ta kula da shi, ama ya zamto har mutanen da suke bayi a gareta sunna neman yi mata katanga da haka dan ta zubar da hakan ta yi watsi da shi wa wasu? Har ake ce mata fatarta ba ta shiga kicin bace dan aikata aiki mafi hatsari da kaiwa jiki irin na abincin mijinta? A dan kausashen da basu saba ganninta ba ta dubi matar ta ce" Jayaya kike yi da umarnina?" Da sauri ta sada kai, ta sake dukawa tana mai neman afuwa Da umarni ta ce" ki rike magiyarki!, Ki maida hankali kan abinda na saka ki, sannan ki je dakin sako a rubuta takardar gayata cin abinci a falon mai martaba, karfe takwas na dare, a turawa SARAUNIYA BAHIJA!" Daga haka dakinta ta wuce dayar ta bi bayanta da sauri dan fitar mata da dukkan abinda take bukata Ita kuma a lokacin tana fitowa sai da ta dokawa Umma waya ta sanar mata cewa wai HUZNAH ce zata zo Kicin na bangaren Sultan, A lokacin kuwa Umma bata jima da baro bangaren ba tunda aka sheda NADIRAH ta dawo bangarenta, ta zo tana son jin dalilin da ya sa Nadirar har ta fito ta je wani wajen ba da izininta ba Innar Nadirah kam, uffan bataa ce ba, har Umma ta gama maganarta, hakama NADIRAH kallonta kawai take yi har ta ajiye maganarta, a nan ne ta samu kiran nan wanda ya kusan sumar da ita Da tuhuma ta dubi NADIRAH ta ce" Shekara tara kennan yarinyar cen na masarautar nan, bata taba cewa zata shiga ta yi masa girki ba sai yau da kika je bangarenta? Me kika ce mata?" Da dan kosawa Nadirah dake bale dan kunnen kunnanta ta dubi Umma Lalle matar ta gama samun waje ne gaba da baya, ya zama wajibi kuwa ta bita a hankali har ta durmiyata a cikin ramin da ta haka da kanta Kai ta girgiza tanaiwa idannuwanta wani irin warrrr sannan ta dan yatsine fuskarta ta ce" Kin san menene burina?, Burina na gama abinda ya kawo ni gidan nan, na smau yancina, burina na aikata aikin da ake so na aikata na kama gabana, domin a waje inada rayuwata wace nake matukar son na ga na cika, ni nan da kika ganni burina na yi kudi na gagara, ai ba laifi bane ba kuma haramun bane yar kauye ta yi buri da mafarki ko? Ina iya ranste maki a kan kudi komai sai na aikata, wani yardar tawama dan na tabata za'a bani wani dan abin ko yayane na je na ja jari, ba kowa rayuwa take tafiyarwa ba a cikin daula kin fahimta? Ki yi hakuri zaki ji maganata wata iri kamar na raina ki, aa ba raini bane, kin daga hannu kin mareni ido da ido, ba'a yi min haka, ki sani da ba dan na san jakarki da nauyi ba da sai na maida maki goman wanda kika yi min!" NADIRAH ta ajiye maganar, da wani yannayi da ya saka innarta dagowa tana kallonta, domin tamkar wata rikakiyar yar daba ko irin rikakun yan barikin nan Ita da kanta Ummar shan jinnin jikinta ta yi, a lokacin abu daya ke ranta shine bata kyauta ba da har ta kai hannunta fuskar NADIRAH, ashe yarinyar tanada mafarki nata na kanta, gaskiya ne mai yawo a cikin mafarkin kudi ko mulki baya tsoron kowa, baya tsoron komai, a mutu ko a yi rai du ba shi bane a gabansa in dai yana irgen ta ina kudi zasu shigo Lalle ta yarda yarinyar na iya aikata masu aikinsu, ama duda haka bata ga dalilin da zai saka ta je bangaren HUZNAH ba, har maganar nan ta fito fili haka ba gaskiya Umma ta dan dubi Inna, sai kuma ta sake kallon NADIRAH, ta dan rage gautsin Muryarta ta ce" Kema kin san marin nan dan raina a sama ne, ni na mareki ama ni na ji a zuciyata" Ta idasa tana mai dora hannunta daidai zuciyar tata A dole NADIRAH ta kalli innarta, da sauri kuma ta kalli Umma Umma ta ce" Ama kawai ki yi hakuri, ba za'a kuma ba, yanzu ki fada min me kuka tatauna da wancen ne?" Tabe baki NADIRAH ta yi, sai kuma ta cirw kanta ta ce" idan ta hanyar da nake tunanin za'a bani aikina a gidan nan ne na yi sharar fage, dan ya zamto an samu abinda ake so ba da labe labe ba, dan kuwa in ban samu hanyar yi masa girki ba, hakan ba zai tana samuwa da sauki ba, ina fata kina gane yarena" Wani irin farin ciki ne ya ratsa Umma Har ta rasa me zata ce a irin wannan lokacin Kiran dake ta shigowa ya sakata mikewa ta masu alamun sai ta dawo ta fice domin a cen kicin din ne ale ta kiranta, Kai tsaye ta je, tana jin ba'asin kiran ga mamakin HUZNAH sai Ummar ta bata damar dafawar hankali Kwonce, duda dan abin da ta saba sakawa a irin abincin auta yai ba zata saka ba kennan? Ama zata yi hakuri har gobe Girkin NADIRAH A dakin NADIRAH Umma na fita Innart ta dubeta, da duba irin na karra son gane gaskiyar lamari Sai kuma ta sauke numfashi ta ce" haka nake so, ina matukar son idan kina magana ya zamto tana sauraronki, dan karfin muryarki ya fi nata zafi?, Haka kuma ina fatan Allah ya nuna min ranar da zan rama marin nan, walahi ko ana ruwan mazuru da zaho sai na zabga mata mari in sha Allah, Kwartuwar bamz da wofi, wai zuciya, ina ta ga zuciya wancen?" NADIRAH ta yi murmushi ta zauna tana tunanin idan har hakarta ta cimma ruwa, matarsa zata amshi girkinsa, hakan na nufin za'a rage wata jarabar, idan kuma an kawo maganin da za'a zuba masa a abinci hakan na nufin ita za'a ba ta zuba, ba Umma bace zata zuba abincin ita kuma a bata ta kai masa!, Ko ba komai Abam su Inna za'a dan karra kwanakin shiruftaka bawan Allah!............... Kusan sallar magarib takarda ta sameta ta gayata cin abinci, wanda a kusa kusan nan Umma ta fada masu da wahala ta sake samun zuwa falon UMUGHLUK ITIBEL sai idan ya huce Murmushi kawai ta yi ta ajiye abin tana sake karantar girman girmama abu irin na gidan sarauta, zo ki ci tuwo ne aka buga a computer? Watau tvn nasara? Allah shi kyauta Da dare ya yi sai da larfe takwas din ta kusa ta shige wanka, a nutse ta fito ta bude tarin kayan dake sakata nishadi idan tana kallonsu ta zaro wata doguwar riga irin ta kantin nan ta zaman cikin dakin nan mai laushi mai ruwan fatar kare ta ajiye, sannan ta dauko pant shima fari kal shi kuwa ta ajiye Bangaren alkyaba ta bude ta zuba masu ido A hankali ta dora hannunta ta ringa shafasu tana kare masu kallo A kalla zasu kai talatin ko fi a irgenta,haka kuma kowace da irin yannayinta, watau da tsarinta da kyanta da komai Ajiyar zuciya ta sake saukewa a hankali ta janyo wata mai ruwan gashin mage, laushinta da dukan da ta yiwa kirjinta ya dakata daukota domin tana kallonta sai da ta ji ta sace zuciyarta, haka kuma tana daukota a hannunta ta ji wani laushinta sai da ta lumshe ido tana sauke ajiyar zuciya A hankali ta karasa wajen abin turaren wuta ta dauki abin kyastawar ta ciro ta kyasta daya ta dora ta dan dakata ya kama sosai har ya fara zama toka toka kadan , sannan ta je ta ciro turaran wutar na kaya ta zuba ta loda kayan Wajen madubi ta karasa ta tsaya cike da tunanin me ya dace ta yi? A hankali ta zauna tana dan dora hannunta sama ta shiga tuna maganarta da matar dake koya mata yannayi da lamura irin na sarauta A hankali ta maimaita kalmar da take yawan fadi da yaren nasara, watau CLASSSSS Hannunta ta dan bi da kallo sai kuma ta saki gashin kanta ta dan wana kanta kadan ta sake zubawa madubi ido Cikar gashin da bakinsa yanada yawa sosai, ya ishi bawa kwaliya ko wace iri ce , cen dama ta gaji iya kwaliya da gashinta, kitso ne bata so sai sun sha rikici da innarta take yi mata tafka tafka biyu, ko hudu A nutse ta saka abin tsaga daga gefen hagu na gashin kadan ta yi tsaga mai dan tsayi kadan ta ja gashin gefe sannan ta saka macaji karami a hankali ta ringa caje wanda bashi da yawan har ya kwonta luflufluf, sai kuma ta saka yan yatsunta a na gefen ta dan kara sakashi ya karra tudu kadan ta barshi zube a gaban kijinta da gefen fuskarta kadan Jan baki take ta kallo, da kyar ta iya janyo mai ruwan kasa kasa ta bude shi ta shafa dan kadan a bakinta , sannan ta dauki kwali tana ta kallo da tunanin anya ba sai ta yi kiran innarta ta saka mata ba? Domin bata taba sakawa da kanta ba ai Karshe dai dagewa ta yi ta ringa karkata kai da kyar ta saka kwalin tana tsale da ihun ta saka sannan ta koma wajen kayanta bayan ta ga takwas ai ta gota tuni t dauka ta saka pant din da rigar ta koma wajen madubin tana kallon kanta harda dan juyawa a gabansa kadan ta dora hannunta a saman cikinta dake shafe uwa babu hanji a ciki ta yi murmushi , sai dai tudun duwawunta ne suka bata mamamaki, ba kasafai ta cika kallonsu ba, aminiyarta, kawarta Yar dubu ke yawan cewa ta ringa saka sutura mai rufe jiki saboda maza lalatatu masu bata ya'yan mutane dan Allah ya bata kira, ita kuwa sai tace Aminu zai iya tarda mutun ya kashe shege a kanta Alkur'an! Murmushi ta yi tana gyada kai, idan ta koma ta labartawa yar dubu abinda ya faru da ita bata san ko zata yarda ba, ta yiwu sai ta sakata ta sha Kur'ani ko zata yarda, ama in sha Allahu ko kwana zasu yi sunna dambatuwa sai ta sakata ta yarda tunda ita ba makaryaciya bace bale a mata iya shege Turaruka ta dauka a fili ta ce" Ku zo nan yayan albarka mu bare banza, tunda an zubaku uwa ba siya aka yi ba" Karshe dai ta kai mintu talatin bayan karfe takwas din sannan ta fito da takalmi plat mai laushi ta yiwa Innarta salama bayan ta ja rantsuwar ba zata aikata aiki makamancin na jiya ba sannan ta fice ita daya babu ko yar rakiya ta bi ta babar hanya hankali kwonce tana tafe tana kallon yannayi da tsare tsaren ginnin sarautar ta garin AGADAZ, komai a al'adance sannan da tsarin zamani, kana gannin abin zaka gane an narkar da kudi fa ba abin wasa bane Bata san cewa shiga ita kadai sai ta sha wahala ba sai da ta karasa bangarensa Hanyar ta samu kanta da zubawa ido da tafka tafkan dakarun masu tsaitsaye sunna gadin wajen A lokacin da ta sanar masu itace Bahija amarya aka yi mata tambayar zata halarci cin abinci ne? Ta bada amsa aka nemi da ta bada takardar gayata sai da mamaki ya kamata A nutse ta aro halaya irin nasu, a dake ta bada umarnin a shiga a sanar da zuwanta idan an bada umarnin ta koma sai ta koma A kan dole suka aikata hakan, bayan kamar minti biyar aka bata danar shiga Baki ta tabe a ranta tana ayana' dama na zo da redion innata na saka kidan kai ku kama sana'a mata na maku habaici kitika kitikan banza kunna gafin kato...., Koda yake na san yana dan baku na sakawa na salati' Haba dai ta samu ta karasa ta wuce bayin dake zaune bayan sun zube sun gaisheta sunna mamakin ganninta ita daya kuma amsa masu harda su ya gajiya sannan ta bude madubin dake fitar da danshin AC ta shiga da salama kasa kasa a bakinta Ta tabata koda shi namijin bai kalleta ba, yan matan sun zuba mata ido, domin tana ji a jikinta kallonta ake yi, Wajen da ake sarkafe kaya idan a shigo ta karasa, hankali kwonce ta cire Alkyabarta ta rataya a jikin abin ratayawar, wanda haka sai da ya saka HUZNAH kwarewa da abinda ta saka a bakinta ta dan shiga tari kadan tana sin cire idonta a kanta ama dan jaraba tana karra kallonta Kasa kasa ya dan dago da dubansa daga abincinsa ya dan kalli HUZNAH Sai kuma ya kai dubansa inda take kallo tana fan tari hadi da kai kofin ruwa bakinta Samun kansa da zubawa yarinyar ido ya yi na yan dakiku sai kuma ya dauke kansa a ransa ya ayana' Ta tabata, yar daba ce yarinyar nan, ko irin yan duniyan nan rikaku' Tana murmushi itama a nata ran tana ayana' Haka nake so, so nake na haukataki, ki yi zaman aure da mijinki mai sunna zaman aure kafin na tatara tsumakaraina na karra gaba Alkur'an, ama kina abu kamar wata bagidajiyar da bata da ilimin adini? Ilimi ai haske ne, kuma ko ni da nake kauye a wannan fannin na san me nake yi sarai!' Bata tashi idasa neman rikita masu lisafi ba har Auta da ta karra zarro ido, Uwa uba Umma, matar dake bata mamaki, zaman cin abincin dare da ya dace ace ya yi daga shi sai matarsa a dakinsu abinsu aa, ga wata mai zarro ido kamar mai farfadiya, sai wannan rusheshiyar mata mai ruwa da munafukai a saka su tsakiya, ita kuma matar kai a kasa uwa tsohuwar algunguma a gaban mijinta? Uhum, sam basu da tsari gaskiya sai da ta karaso facing din da yake ta dan kama gefe da gefen rigarta, ta dan baje tsayuwarta kadan sannan ta saki dayan hannunta tana murmushi ta yi wani yannayi da hannun da muryar murmushi tace" Barka da warhaka Aban su Datawa......" Yanzun kam Umma ce ta ji miya miyar zata sarketa, a dan rikice ta cire dubanta daga kan Nadirar ta maida kan abincinta tana yin iya yinta dan hanna kanta sumewa da tashin hankalin da take kallo Auta da du take a hali na rashin jin dadi dan an sakata cin tuwo mai nauyi bayan ita bata cika son tuwo irin haka ba , asalima nonon sanuwar dake cikin katon flask na yayanta take so a zuba mata, ama Umma tace wannan zata ci dan maganinta sai ta samu kanta da sakin boyayan murmushi tana sake satar kallon yayanta da abin al'ajabi irin na mahaukatan zamani ya saka shi dafe haba a bayane, duda rawaninsa iya bakinsa da habarsa kadan ya bayanar yana kallon rikakiyar yar gajaliyar nan Dagowa ta yi tana fadin" Kai kuguna" Sai kuma ta karasa ta kalli HUZNAH ta sakar mata murmushi a takaice ta ce" Sannu fa" Sai kuma ta kalli Auta itama ta zarro mata ido yadda take ta zarro mata ta ce" Ke kuwa gyara dubanku mana haba" Sannan ta sake kallon Umma, ta sakarwa Umma murmushi wace idannuwanta tamkar zasu fado dan kallo itama a takaice ta ce" Sannu dai Ummanmu" Kujera ta ja ta zauna tana sauke numfashi irin ta sha aikin nan sannan ta ce" Walahu nake fada maki aunty dan kwali na nema na rasa karshe dai haka na taho kar aje na yi lati 'Latti? Dan kwali? Ya Allah ka sakani gane wannan mata tun kafin ta kasheni, wannan wace irin mace ce? Wani lati bayan sai da sarki ya zauna ta zo?, Wani dan kwali a tarin suturunta?, Ta rasa me zata saka sai wannan rigar?, Ta zo ta mana gaisuwa kamar sa'o'inta? Koda yake shima sarkin ga yadda ta gaishe shi uwa uba Umma?, Ya Allah menene wannan ne? Wacece wannan matar ne? Allah ka shiga lamarina da ita ya Allah ka dorani saman kanta kar ta rikita min zamana, ni dai banida matsala da ita, ama sai wani haroni take yi!' HUZNAH ta ayana a ranta sannan ta dauke kanta bata ce mata komai ba, dan baya so ana saman table a ringa yawan magana haka Baki NADIRAH ta tabe, ita fa ba fa za'a yanka mata baki ba har ya zo yanai mata tsami dan bakin hali da rainawa kai wayo ba walahi, tsaf bakinta na magana ne Allah walahi Abincin take kallo Kaf abincin nak babu abinda ya yi mata, ba cika son abinci ta yi bama a rayuwa, hakan ya sa ta fara yin tsuru tana kallonsu daya bayan daya ta ga dai abinci kowa ke ci banda Auta dake dan fama da nata ta kasa ci da kyau A hankali ta ce" Bakya son tuwon ne?" Auta ta dago da sauri ta kalleta, a hankali ta saci kallon sauran, gannin babu wanda ya kalleta sai ta amsa NADIRAH da ido NADIRAH ta dan karra kallonta ta ce" To ki bari mana ko dole ne?, Kina wani abu kamar an wanka maki mari" Umma ta dago ta zuba mata kakausan kallo kafin ta budi baki a sanyaye ta ce" Allah ya karra maki lafiya, i ya zama dole ta ci abinci dan ta sha maganinta" NADIRAH sarai ta karanci sakon idannuwan Umma, ama sai ta watsar Hasalima mikewa ta yi ba kwaramniya ta shiga dan bubude abincin tana rufewa, yannayin da take yiwa fuskarta kamar ta ga wani abinda bata son ci mai warin nan ke karra kunna HUZNAH Karshe ta maida dubanta kan abubuwan dake gabansa A soyayarta da nono ko a me aka saka shi kallo daya zata yi masa ta gane menene Murmushi ta yi ta dauki manyan kofuna na kwalba biyu ta ajiye ta mika hannu ta dauko nonon da ake tofe masa da addu'a daga wajen SHEIK sannan a kawo, nonon da ko Umma bata tabawa bale HUZNAH, ta bude ta cika a kofi daya ta mikawa Auta sannan ta cika a daya tana murmushi ta rufe ta koma ta zauna ta sake kallon Auta ta ce" Ki ajiye abincin sai ki sha wannan, yanada anfani sosai ga lafiyar dan Adam" "A kan wani dalili zaki taba abin madarar mai martaba?" Muryar HUZNAH, da yannayi na ta fara hasala ta yi maganar Kafin HUZNAH ta sauke harufanta Umma ta dauki nata itama a dan hasale ta ce" A kan wani dalili zaki saka yarinya ta sha madara bayan tuwo nace ta ci ta sha maganinta ne?" Idannuwansa ya rintse, hayaniyar ta farra hawa kansa, jira yake ya ji ta yi magana a haukacen da ta saba, sai ya ji shiru Hakan ya saka shi dago dubansa ya shiga binsu da kallo su dukansu Su amsa suke jira daga gareta Ita kuma ta dauki madarar da aka mata magana a kanta dan bakin rashin ji ta kai baki ta lumshe ido tana shanye masa madararsa, madararsa fa, shi fa, shi ASADEEK jama'a Rasulullah (S.A.W) 🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ NADIRAH kuwa a ranta ayanawa take yi' ku bari na sha na dawo hayacina, sai mu baje idan hali ya kama, ai ba'a gwa da gwa da yinwa kawuna uwa dutsin jifan shedan!' Tashin hankali, ita bata san me ake nufi ba hala? Mun shigesu🥺🥺🥺🥺 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣3️⃣ Sai da ta gama shanye madarar nan, ta lumshe ido tana jin yadda take ratsa mata kirjinta, watau sanyi ne da ita madarar, tana matukar son madara mai sanyi ama innarta sai tace aa in dai zata sha ga mai dumi kawai ta sha Idannuwanta ta bude hankali kwonce ta sake mika hannu ta dauko dan tsinken sakace hakori kamar wace ta ci naman kazi ta dan bude bakinta kadan ta tsatsaka sai kuma ta yi wani tsut tsut da bakin nata sannan ta barshi a ciki tana dan wasa da shi a bakinta A wajen nan Auta ta fi kowa jin kamar zata kurma ihu, domin tun kallon na mutun biyu ne har ya dawo na mutun uku sunna kallonta, amsa suke jira ama NADIRAH ta gama ta yi shiru abinta da bakinta Umma, ji take yi, wani irin ashariya, irin na maguzawa, irin na mutanen kafurci na mata yawo a harshenta, so take ta yiwa yarinyar nan abinda bata taba tunanin ana iya yiwa mutun a duniya ba, sai dai wanzuwar UMUGHLUK a wajen ya sakata kasa barkata hakan Ajiyar zuciya NADIRAH ta sauke ta kalli HUZNAH dake kallonta ta daina cin komai Murmushi ta yi mata ta ce" Aunty, ba'a taba madararsa ne? Ko nice ban zama ta gida ba?"........... Sai kuma ta kalli Umma ta ce" Umma, magani ai idan an sha madarama ana iya sha ko? Bata ra'ayin cin tuwon idan aka takurata sai ta samu matsala ai inaga ko?" "Ba maganar kasancewarki yar gida ko yar wajen gida bane, babu mai taba madararsa, yaya zaki taba baki tambaya ba kanki tsaye"...... HUZNAH ta fada tana dake fuskantar Nadirah Ko ajiye maganar bata idasa ba Umma ta ce" Bama wannan ba, maganar cin abincin Auta, shanta, komai nata nice a gidan nan, babu macen da zata shigo ta shiga ciki domin nice mamanta, kin gane? Kuma rashin lafiyarta dole ta ringa cin abinci a kai a kai " HUZNAH ta sake cafewa, dan bata ga a kan me Umma zata hannata fadin nata damuwar itama ba, a birkice ta ce" Aa Umma, ai dolene nima na fada mata ta gane cewa madararsa, abu ne mai matukar mahinmancin da shi kadai ke shan abinsa, ko ke bakya tabawa, haka nima, ta zo ta dauka ba izini ba komai ta sha ta ba Auta?, Ai ba haka ake yi ba, ba wai maganar tana matarsa ko yar uwarsa bane, a gidana ta sameni dole zata bi takun tafiyata!" NADIRAH ta sake waro ido wata shegiyar dariya na tukota, a hankali ta kai hannunta wajen bakinta ta furta" Toh fah" domin abin ya bata mamaki ainun, bale da kamar hayaniya da yar cacar baki ke neman kaurewa a tsakaninsu, hakan ya sa da sauri auta ta shanye madararta tana sake kallonsu itama NADIRAH ta kalli wannan, ta kalli wannan mamakinta ya ki barinta, gaba daya sai ta samu kanta da raina masu ajawali walahi Kamar daga sama, muryarta a tausashe ba a kausashe ba ta ce" Ku dan dakata ku huta mana, abin nan dai tunda ba sabon Allah bane ya dace ku saurara hakanan gaskiya, na gama fadin amsar kawai a wuce wajen mana, karawama zan yi!" Sai da Umma ta ji zata kifu a sama, da karfi ta ce" Lah ha ila ha ilalahu......." Kara talabe haba ya yi a bayane, kasa kasa sosai ya tare da fadin" Muhamadu Rasulullah salalahu alaihi Wa salam" Umma ta nunata da yatsa ta ce" Babu abinda zaki karra a nan, yaushema kuka shigo da zaki nemi fin yan gida?, Dokata babu mai taka min domun ba zaki taba fina sonta ba, yarinyar dake fama da ciwon hauka ne zaki saka ta kwonta da dan ruwan madara a cikinta da magani?"......... Tunda ta furta kalmar nan, sai ASADEEK da HUZNAH suka zuba mata ido, kalmar haukan da ta ambata kai tsaye ba wani dan sakaya ya saka su zuba mata ido su biyun, Auta kuwa sai ta samu kanta da sada kai bata ce komai ba NADIRAH ta zuba mata ido itama, kallon da take yi mata ya dan ankarar da ita cewa a yau ta so barin bacin ranta fitowa, uwa uba itace har da yin hayaniya a saman kansa bayan basa yi masa haka, hasalima abinda ya sa ta ci galabar sace zuciyarsa dan ta kasance mai tausasawa a gabansa, sam bata wasa da yarda da yin hayaniya a gabansa, shi yasa baya taba daukan maganar Auta dan ita da koke koke, da hauka haula take son ganar da shi, har kwanan gobe, shi yasa a kulun yake yi mata kallon da Umma ke nusar da shi cikin hikima Wata wawuyar ajiyar zuciya ta sauke ta dauki tissu mai girma ta shiga goge fuskarta, sannan ta koma ta zauna Kanta ta sada, ta rage muryarya sosai, kasa kasa ta ce" Allah ya huci zuciyarka, na nemi zurmawa dan bana son na ga wata fitina ta billo a cikin gidanka, mu barka da rigingimun cikin gari da na wajen gari mana? Ama sai abu ya nemi bilowa, ina son dakushewa ne dan kar Bahija ta yi aiki da isa da takamar ita yar uwarka ce ta kawo mana cenji a zamantakewarmu, ba zan lamunci haka ba, idan har na bata maka ka yafe min, na tuba ba zan kuma yin hayaniya a gabanka ba" Ta idasa tana karra sada kanta sosai, wanda hakan ya saka Auta kafeshi da ido tana ta yin magana da idannuwanta ama baya gane komai, sai kwalar da ta cika mata ido da ya iya gani kawai A hankali ya gyadawa Umma kai, hakan ya sakata sake sadawa ta furta" A tashi lafiya" Daga haka ta fice ta bar falon tamkar zata tashi sama ta kuma nufi bangaren NADIRAH Shiru ne ya karra biyowa baya, na yan dakiku Cike da darajawa, da girmamawa HUZNAH da bata taba kamanta irin haka a rayuwarta a gabansa ba ta sada kanta itama tana share yar kwalar da ta tarun mata a gurbin idannuwanta Ta rasa me yasa, ko kallon yarinyar ta yi sai ta ji wani katoton kaho ya tsaye mata a kirji, uwa uba irin abinda yarinyar ke nunawa , yayama za'a yi ta zo jiya jiyan nan ta nuna zata koya mata zama da mijinta? Yaya za'a yi ta zo jiya jiya ta zauna a kujerar da ta fi kusa da mijinta sannan ta dauki madarar UMUGHLUK ITIBEL ta sha har ta yi kyauta? Da kyar ta iya hanna kanta yin kuka, muryarta a raunane ainun ta karra sada kanta ta ce" Allah ya huci zuciyarka, Allah ya karra maka lafiya, na bari abinda nake gannin duhu a gareni neman rufe min ido, lamari ne na halitacen abinda ban isa da shi ba a zuciyata, in sha Allah zan kiyaye gaba,.....zan je bangarena na yi shafa'i da wuturi, Allah ya tashemu lafiya" Kallon abar sonsa yake yi, kallon matarsa mai laushi da nutsuwa yake yi, sosai ya yi mamakin gannin ashe ta iya fada?, Sosai ya yi mamakin gannin an hasalata da wuri haka, yana kallonta ta mike da idannuwanta da take tare hawaye ta sake rufa alkyabarta sosai ta juya ta bi ta dayar hanyar nan domin ba zata bi ta kofar shigowa ba bayi su fahimci halin da take ciki Tana tafia wajen ya rage su uku kacal NADIRAH ta yi wuki wuki ta kalli wannan kujerar ta kalli wancen, watau kujerun Umma da HUZNAH, sai ta ji kamar wajen yanzu yana neman yi mata yawa, dazu kuwa da abokan hamaya wajen har kadan ya so yi mata, dan so ta yi a yi ta yin rikicin har safe "Kin san daraja da girman uwa kuwa?" Ta tsinci wata murya, mai cike da kamala, da nutsuwa, uwa uba da kaifi a zuciya ta daki kunnenta A hankali ta juyo ta kafe fuskarsa mai dauke da rawani ido, a yanzu ta karra yarda da taken gadonta da ake yiwa maza, watau buzu babu rawani gwara babu wando (😁🙄), in ba wannan ba, menene ta kangama rawanin a cikin dakinsa, falonsa, tare da iyalinsa? To shi yana cire rawanin nan kuwa? Sai kuma ta samu kanta da sake dora dubanta a wajen da shara sharan rawanin ya fi yawa, sam fuskarsa ba yaba yaba irin ta tsufa, to ama me yasa ake ce masa Aba? "Ita uwa, itace halita mafi daraja a duniya, ita wannan da kika yiwa rashin kunya tamkar uwa take a wajenmu, kin san darajar uwa kuwa?" Ya sake ambata a tausashen da ya sakata lumshe idannuwanta ta mayar da jikinta ta jinginar jikin kujerar sannan ta sake bude zaburarun idannuwanta ta zuba a fuskarsa A rants take ayana magana kamar haka' Sannin darajar uwa, ya sakani fadawa a bakin kura, sannin darajarta ya sakani tarban aradu da kai, sannin darajarta ya sakani juya baya na baro wanda nake so dan zuwa na rayu da bakin rayuwata, sannin darajarta ya sakani zama tamkar gimbiya bayan ni ba kowa bace face mutun dan Adam, ka sani da ban san darajar uwa ba, da yanzu wata maganar ake yi ba taka ba!' Auta dake kallonta, ji ta yi kamar ta bude bakinta ta koya mata dukawa da bayar da hakuri, ji take yi kamar ta girgizata tace mata hakuri ake bayarwa gaba daya cikinta har wani kuuuuu yake neman yi gannin Bahija ta ki cewa uffan bayan yayanta na magana yana kuma son amsa ne Kakausun idannuwansa ya lumshe, yana danne zuciyarsa dake tunzura da sake gannin tsantsar rashin kunya a tare da ita Dubansa ya maida kan Auta, ya fitar da hannunsa mai dauke da birda birdan jijiyoyi masu girma da nuna halitar girma ya ce" Bana son abinda zai taba min ita, haka kuma bana son abinda zai taba min matata, ki kula kin ji......, Yayama sunnanki?" Auta dake wuwulga idannuwa ne ta budi baki a hankali ta ce" Abah, dan Allah ka yi hakuri ka ji? Sunnanta BAHIJA" Kakausan kallon da ya wurga mata ya sakata sada kanta sosai tana sauke ajiyar zuciya Bai ce komai ba ya mike ya nufi falonsa ya zauna cike da wani irin tukuki shima na haushin Yar, wannan yarinya ai yanaga da ya samu haihuwa da ya nasota duniya, ama dan iya wulakanci da girmansa, da darajarsa ya ringa magana kamar zai ari baki tana kallonsa ba amsa? Zai yi maganinta ne, abu daya ya hannashi babalata maganar CHEIK walahi! Bayan tafiyarsa, NADIRAH dake kallon Auta a hankali ta ce" Ya tafi fa, ki dago kanki" Da sauri ta dago tana kallon NADIRAH, sai kuma ta rafka tagumi ta ce" Yaya na magana bakya bashi amsa?, Innalilahi aunty Bahija bakya tsoronsa?" Maimakun NADIRAH ta bata amsar nan sai ta kafeta da ido, a hankali ta ce" Tun yaushe yake maki kallon mahaulaciya, me yasa kila yarda ake maki kallon wace bata da hankali?" A zabure Auta ta sake kafeta da ido, wannan karron har hannunta na rawa sanadiyar bugawar da zuciyarta ta yi, tana kallon NADIRAH, NADIRAH na kallonta Muryarta na rawa ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣4️⃣ Muryarta na rawa ta ce" Yaya aka yi kika gane lafiyata kalau?" NADIRAH ta yi shiru tana kallonta, bata san me zata ce mata ba, bata san ta inda zata fara ce mata komai din ba Ajiyar zuciya ta sauke tana dan kawar da dubanta daga inda suke ta hango falo, a zaune yake yana operat din computer , hankalinsa baya kansu kwata kwata A nutse ta karra fuskantar Auta , wannan karronma ta ki bata amsar tambayarta ta dubeta ido cikin ido ta ce" Idan shekaru suka fara ja, ko ba'a yi maka aure ba, ko iyayenka da rai, zaka zamto nama a gaban mahauta, idan na ce maka mahauta ina nufin du wani wanda numfashin da kake shaka a duniya ne ya zamto masa abin jin haushi da tsana a rayuwa, shekarun da suka hau kanka, ko nisa da iyayenka zai zamto ne ana wawurarka ba ji ba gani, idan har ka zama komai ka labe ko ka saki kuka yagalgalalen nama kake wanda kowani wawa zai wawura ya ce zai iya siya ya ci, ban ce maki wane ne makiyinki ba, ban kuma san kowa a cikin masu sonki da bataciyar rayuwa ba, ban san me kika rayu a cikinsa ba, ban san me kike rayuwa a cikinsa, ban san girman tsoron da kike yiwa koma menene ba, ban kuma san me yasa kike tsoron abin har haka ba, abinda na sani shine, babu bawan da ya isa ya tsalakewa kadararsa, kuma babu bawan da ya isa ya ja da hukuncin ubangiji, ka rayu kawai ba dan ka birge wani ba, ka kuma tuna da mutuwa da tsayuwa a gaban ubangijinka, wasa kike yi da sallah? Ke din mutun ce mai shagwabar da kika kasa jajircewa rayuwarki, ko me ya mayar da ke abinda ake dubanku kina da damar kaucewa, rashin sannin mafaraucinka shine matsala, idan har ka sani wayance masa zai fi komai zama abu mai sauki, kin ga ba fa fito na fito ake yiwa kowani mafarauci ba, dan wanin mashinsa ta fi karfin ya harba bai samu nama ba, ama ana iya yin wayo a gudu, harma a kama shi a cikin tarkonsa.........., Babu abinda na sani, ba kuma na son sani, a ganina bai cencenci ki ci gaba da rayuwa kamar wata yar tatata ba, ki yi aiki da iliminki dan tsira da mutincinki!" Daga hala NADIRAH ta muke ta shiga tatare kwanonin nan tana nufar hanyar da ta tabata ko yayane a nan zata samu kicin Ai kuwa a nan din ta samu kicin din da ta zama kamar mahaukaciya wajen kallo, domin kafin ta fito sai da ta sha kallo har kamar zata kwana a wajen Kayan ta ringa kwashewa tana kaiwa, sauran madarar da ba'a sha ba kuwa ta tsiyaye a kofi ta sake kafa kai ta aikata sannan ta kai kofin ciki ta fito ta nufi falo hankali kwonce dan tafia A zabure Auta ta mike daga zaunen da take, kamar an tasheta a barci ta biyo bayanta da sauri tana fadin" Aunty, Aunty, Aunty BAHIJA " Har ga Allah bata tsaya ba dan ba sunnanta bane BAHIJA sam bata gane da ita take ba sai da ta karasa ta ciro alkyabarta ta ankara itace BAHIJA fa, hakan ya sa ta juyo tana murmushi ta ce" Ni ba zakina ce min Mama ba?" Rubutun da yake yi a computer ya dan dakatar , tunda Auta ke kwala kiran nan ya bisu da kallo har furucinta da ya saka shi jin kamar ta gaura masa mari, Mamah?, Sai ya samu kansa da dagowa ya dan zuba masu ido, zai iya rantsewa Auta ta girmi wannan abar, ama ta dubi idannuwanta tace ta ce mata Mama? To a kan mema? Itama Autar abinda ke ranta ta dan kawar tana dubanta ta ce" Mamah?, To ke ba auntyna bace?" NADIRAH ta rage murya tana dage girarta daya tak, dayar kuwa ta yi kasa da ita ta ce" yo mana, matar Abah ba mama bace?" Auta ta saka hannunta ta rufe bakinta tana yar dariyar da ta saka yayanta kureta da ido, Sai kuma ya saukar da dubansa kan hannayensu, a lokacin da NADIRAH ta saka Alkyabar ta ja hannunta ta ce" Mu je " Maimakun ya ga Auta ta kiya, kamar yadda take yi a lokuta da dama idan yace ta je Umma ta rakata, ko yace ta je HUZNAH ta rakata, sai ya ga ta yarda a bakuwar fuska, ko dan ta ji ance har uwarsu ce zata saki jiki da ita?, Subahanalah idan haka ne kuwa ya zama wajibi ya dauki mataki da wuri wuri, domin ba zai yarda ta saki jiki da matar da ba ita bs, ajema zuwa ta yi ta cutar da ita a banza a wofi, gashi Auta ba lafiyar kirki ba ta yarda da ita a banza da wofi Yana ji yana gani suka fita, hannayensu rike da junna, bai hanna ba, bai yi ihun da yake ji yana son masu ba, ya kame girmansa ne dan kar ya cika hayaniya a gaban yarinyar ta raina shi, rainin da ta yi masa a yanzuma ya isa, ama in sha Allah a gobe zai yi kiranta daga shi sai ita ya ja mata kashedin da zata fahimta, ko da me ta zo ya fita iyawa, ya sarara mata ne dan ance ya saurara, da ba dan shi ba ta yiwu da yanzu tana kurkukun azalumai! ___________________________________ "Ta yaya zan iya ganar da yayana ni ba mahaukaciya bace?, Dan Allah ki fada min?" Auta ta fada a lokacin da suka karasa bangarenta NADIRAH dake bin falon da kallo, bai cika hayaniya ba, haka kuma da dan kwaliya irin na yara ƙanana, kayan dakin dai gasunnan dai, tarkace sai hamdallah Kallonta ta yi da mamaki ta ce" Haka kike son dakinki ya kasance ne?" Auta ta bi dakin da kallo, kai ta girgiza ta ce" Umma ce ke sonshi haka, wai tace tunda baki da hankali a zuba min abubuwam yara zan fi sakewa, kuma du ta cire hotunan iyayenmu tace a boye kar su ringa rikitani" NADIRAH ta gyada kai, zuciyarta cike da mamakin matar da makircinta Kasa kasa ta ce" Ki duba ki gani, kina iya sakawa a cenza maki kayan, a hankali kuma sai ki san ta yadda zaki biyowa yayanki, dan ni ba sanninsa na yi ba ai kin gani, ama abinda zaki fara yi shine daina hadiye maganin nan, idan an baki, ko waye ya baki, ki makale shi a kasan harshenki ki sha ruwan ki faki ido ki cire, ai kin fahimta ko? Kuma gaskiya ki daina irin kallon na kamar mai farfadiya inaga harda shi da kike yiwa yayanki ya yarda kin tabu" Murmushi ya subucewa Auta, domin a yadda Nadirah ta fada din abin murmushin ne A hankali ta zauna ta ce" Dan Allah ki kwana a nan kin ji?" Ido NADIRAH ta zarro, sai kuma ta girgiza kai ta ce" Innata na jirana, kun ga, sai da safe" Daga haka ta fice, tana fitowa sarai ta hangi mace ta yi saurin bada baya, irin daga tsaye da take tana hangen bangaren AUTA ta juyar da bayanta Baki ta tabe ta yi gaba, itama ta yi kamar bata gane komai ba ta nufi bangarenta, a zuciyarta tana cike da tunanin wata jarabar na cen tana jiranta Ajiyar zuciya ta sauke har ga Allah wani lokacin tana jin kamar tsoro na son kamata , sai dai kuma in ta ga zalunci karrara sai ta ji bata tsoron uban kowa! A hankali ta bude bangaren nata bayan ta yi salama tana sake kallon dogaran dake gadin bangaren nata, A yanzuma, ko idasa rataye Alkyabarta bata yi ba, ihun maganar matar da ta tabata dama tana jiranta, da tasowarta a hargitse da nufin maimaita haukan da dakikin kanta ke bata cewar zata ci gabaa da cin bilis ya sakata juyowa a zabure, a lokacin ne kuma Innarta ta fara saka hannunta bayan ta sha gabanta ta tare marin da ta yi niyar sake kwada mata Da sauri NADIRAH ta zagayo ta tare hannun Umma da ta so sauke wani marin a fuskar Innarta Rai bace ta ce" Menene haka? Me kike son aikatawa ne?, Ki nutsu walahi kar ki aikata abinda zai zamto maki dana sani ba, domin da wahala hannunki ya kai kasa ban rama wannan ba gaskiya!" Da karfi ta warce hannunta, a harzuke ta ce"Kina nufin ki mareni?, Ki fada da bakinki kina nufin ki mareni? Da kaf danginki sai na karar da su da hannayena walahi!" Abin mamaki, tar ido cikin ido NADIRAH ta ce" Da gawarwaki sun amsa kiran ubangijinsu kennan?, Ina mamakin yadda kika kawo warhaka a gidan nan a zuciyar mutane da yawa, ko dai a kanmu ne bakya iya boye halinki? Karara nake karantarki, sam baki iya takunki ba, ko sunne idannuwansu ya rufe suke ci gaba da maki kallon da suke yi maki? Abinda na sani shine, rashin hakurinki, da zafin zuciyarki zai kai ki ya baro ki!, Na fada maki ba lale bane na ringa zuwa ina fada maki shirina!, Yayama kike so na iya aikata aikin da ake so na yi ba tare da na saba da shi ba? Ke bakya so a zargi uwar gidansa ne? Dan Allah ki saka ido ki sarara min na gabatar da abinda nake son gabatarwa, in da hali in kin san zaki ringa manta cewa tafiyarmu daya in ina aikata wani abin ki daina zuwa inda nake idan muna zaune da su!, Magana ta karshe itace, ki kula da hannunki, in ya sauka a jikina yana iya wanyewa lafiya, ama ba a jikin wannan ba, bana tunanin an yi halitar da zata daketa ina waje na kyale!, Shegema fa ya san iyayensa!" Daga haka ta yarfar da hannun ta nufi ciki rai bace, walahi sai da ta ji kamar zata hankade banzar nan, ita komai na hauka da karambani? Bata yin komai a ilimance? A yadda ta sako burin nan ai sai ta dan ringa nuna tanada kwakwaluwar cin zalin din, gaskiya tama rainawa ASADEEK wayo da wannan matar ta iya rufemasa ido har zuwa yanzu du iliminsa da ganno mai laifinsa? Mtssss! Tana shigewa Hindu ta yi iya yinta dan zaunar da Ummah A nutse ta fuskanceta ta ce" Hajia, ya dace zuwa yanzu mu yi abin fahimta, magana ta fahimta wace zamu fitowa junna a mutun, zan so ki gane, wannan hargagin da rikicin babu inda zai kaimu sai mu falasa kanmu, mu tonawa kanku da kanmu asiri, UMUGHLUK ITIBEL fa ba mahaukaci bane, ba makaho bane, ba kuma yaro karami bane, kuma ke kika raini abinki, kin fimu sannin idan ya fara fuskantar lamari irin na rashin yarda zai iya dora ayar tambaya a kai, yarinyar nan kuwa da kika gani abu daya zuwa biyu zai iya sakata ta tona lo meye kowa ya shiga uku, Hajia ita ba baiwa bace, iyayenta suke bauta, kin ga a dole yannayi na sada kansu a taka su ya sha bamban, sannan tanada ra'ayi nata na kanta, wanda ya saka take iya dubanka tace ba zata yi abu ba, ko bata son abu, to irin wannan abin yanna sakawa a sha wahalar zama da mutun, mutun mai ra'ayin kansa inaga ko a bariki yanada wuyar sha'ani, ba'a juya shi yadda aka ga dama, HAJIA tunda ta yarda aka yi wannan abu da ita inaga mu bata damar da zata aikata aikinta ta hanyar da ta ga zai fi gyarata, ba mu hannata sakat ba ta hanyar saka mata ido a dukkanin motsinta da neman hannata rawar gaban hantsi, ki sani, bata shigo gidan nan dan ta gaje ba ko dan ta kwace maki wajenki, idan kika yi hakuri gyaranku ne ku duka , watau in kika bata dama kika dauke kanki shiga jikinsu ba dan ta lalata mana aiki bane, Hajia na san baki taba ce mana da bakinki kina cikin tsarin gannin an kawar da shi ba, ama mu ba makafi bane, ba kuma mahaukata bane, bokon ce kawai bamu je ba, ama mun rayu da sannin me yake faruwa a tare da mu, ba gardawan yan kauye kara zube muke ba Hajia, haka kuma muna kishin kanmu, wannan gigi naki na daga hannu ki kawo kusa da mu matsala ne baba, idan ya zamto mun fara cin kanmu da kanmu ba zamu ji dadin tafiyar ba, shawarmu kanta na iya zuwa ba daidai ba, kin ga a haka ba dadi ko?" Umma ta ja numfashi, idannuwanta da suka cenza kala da jikinta dake rawa na bacin rai da fargaba ta dubi HINDU ta ce" Ta yaya zan yarda fakat daya cewa ba ni take son zurmawa ba?, Kin ha abinda ta yi kai tsaye, abin mamaki komai bai ce mata ba?, ASADEEK yanada zafi sosai fa, ama take shige masa hanci da dukunkunne?, Ina fata ba kokari take yi idan ta aikata aikin ta sakayani a ciki ba, domin a yau ta saka na yi abinda ban taba yi ba a gabansa, watau hasala da daga murya!" HINDU ta yi boyayen murmushi, a bayane kuwa ta sake kausasa yannayinta ta karra tabatarwa Umma cewa ta fa yi da aniya, in ba haka ba zata iya saka su a halaka baki dayansu! Da wannan ta karra rufe Umma har ta mike ta tafi Bayan ta tafi ta je dakin NADIRAH Saman salaya ta sameta tana jan carbi dan haka ta zauna tana jiranta har ta gama ta shafa fatiha sannan ta mike ta karasa tana shagwabe fuska ta ce" Innata na kwari cikina da yawa, dubi tumbina ya cika makil walahi" Murmushi innarta ta yi tana cewa" To ai na ga kin yi sallah zai ragu, tunda itama motsa jiki ce" Jikin imnarta ta lafe tana sauke ajiyar zuciya Innarta ta dubeta a sanyaye ta ce" Indina, me ya faru yau?" NADIRAH ta dago a hankali ta zuba mata ido, sai kuma ta sakar mata murmushi ta mayar da kanta ta dora a hankali saman cinyarta Muryarta a tausashe ta ce" Abinda na fahimta shine, muguwar yarda, kauna irin ta haihuwa, kusanci mai girma, yarda gaba da baya da ya dauka ya dora mata, bashi da darr ko dari dari a kanta, ransa nan take yake bacewa idan aka tabata, a kanta yana iya yi maka komai, domin yana kiranta da Mamah, mamansa, innata a uwa yake daukanta" HINDU ta lumshe idannuwanta cike da tunani Muryarta a raunane ta ce" In kuwa haka ne, juye mata aniyarta zai zamo aiki mafi wahala a gabanmu" NADIRAH ta ja numfashi itama ta dago ta ce" Innata, jan aiki ne mai wahala, sai dai na fara hango matakin takawa dan karasawa cen, kanwarsa, watau Auta itace matakina, dan kuwa a soyayar tasa da Umma na hangi ta Auta ta maketa, da Auta zan jingina dan ya fara gane yarena, da ita zan jingina dan ya fahimci kumurcin dake tare da shi, domin Innata , Auta da kike ganni, hankalinta rasss, tana dauke da miki ne a tare da ita, da sharin matar cen, ta san yadda ta ci karfinsa har ya yarda cewa kanwarsa mahaukaciya ce, take rayuwa a haka, a zaman da muka yi, na fuskanci shi kadai ke makance da lamarin Umma, domin matarsama bata wani yarda da ita ba, ama kuma bata san girman sharinta ba, a tunaninta kiyaya ce irin ta wasu iyayen mijin, sai dai kashhh, wanda yakeda mahinmancin ne ya yarda da ita, sosai akoy aiki Innata, akoy gagarumin aiki" Ajiyar zuciya Inna ta sauke, a hankali ta ce" in sha Allah, sannu sannu bata hanna zuwa, ita kuma wancen da izinin Allah sai mun kaita kass, sai halinta ya fito karara a gabansa, wanda take dannewa idan tana gabansa na tsayin shekaru, ba an fara yau ba?, Yanzu muka fara!" Da wannan suka yi ta tataunawa da wasu shirye shiryensu hankali kwonce dan su cinma manufarsu! ___________________________________ Dawakai ne kwara biyar, tafka tafka irin ginanun nan masu ji da karfi da isa, sunna tafe sunna sakin huci da abubuwan adon dake jikinsu yana bada sautin cas cas cas Su biyar din dake saman dawakan dukkaninsu manyan mutane ne masu daraja da fada a ji, a cikinsu UMUGHLUK ITIBEL ne a tsakiya, SHEIK a gefensa, sai rikakun yan siyasa, yan kasuwa, sannan jinnin sarautar a gefe da gefe sunna tafe a nutse tafia irin ta ziyara a asibitoci da sanyin safiyar yau, haka kuma sunna tataunawa kan babar Sallar BIANU da bugaje ke yi du shekara shekara SHEIK ya dubi ASADEEK yana murmushi ya ce" ina fata wannan shekarar , iyayen talakawa zasu yi nasu taron da zaman gaisuwa?" Linzamin dokinsa ya rike ya dan ja, hakan ya saka dokin tsayawa, sannan ya juyo barin Sheikh ya dan zuba masa ido Kai ya kada sannan ya kalli gefensa ya ga sauran sunna dan zantawa ne, sannan dogaransu sun barbazu ne sunna tare mutanen dake son yi masu cincirodo Kasa kasa ya ce" Madarata fa , madarar da kake yi min tofi kulun a jiya ban shata ba" Da mamaki Sheikh ya dube shi ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣5️⃣ Da mamaki da kula SHEIK ya ce" Subahanalah, kar dai ka ce min zubewa ta yi?, Ya salam, aya, ka san jiyan nan irin adu'o'in tsarin da muka yi kuwa?, Dan abinda ya dan tunkaro mun nan ko wajen zamanka bi'izinillah daga jiya kulun sai mun masa zama na kansa, dan in mutun ya fi karfinmu bai isa ya ja da ayar Allah ba" Talaicin da ya tuko shi ya saka shi gyada kai ya sake dan taba gefe da gefen cikin Dokinsa, hakan ya saka dokin sake dagawa suka ci gaba da ziyara, ziyara ce ta ba zata, ba a motoci ba, ba sanarwa, sai sun zo kofar wajen a bude masu, a ziyarar su babu inda basa lekawa, a haka suna kara bada talafi sannan sunna gannin sake na wasu likitocin ana rubutawa domin zai yi zama da su ne na musaman Sai da suka gama suka fito dogarai tari guda sunna karra sakin hanyar dan a basu waje su wuce har suka karaso makabarta Sauka suka yi a kafafuwansu suka shige, ADU'A sukaiwa mamata sosai sannan suka ga irin gyare gyare da sharar da za'a yi a makabartar, wasu kaburan sun bude kadan haka, wasu kasar ta baje dai da sauransu,nan ya bada umarnin a saka sanarwar ranar lahadi ana gayata dan a zo a yi gyaran gidan kowa, gidan gaskiya, du wanda yake da lokaci da talafin da ya samu ko menene ana maraba da shi, a saka a redio da TV, a haka har suka gama suka sake fitowa, abokan tafiyar tasa sai da suka masu rakiya har masarautar sannan suka tafi Ya kasance saura su biyu ne a saman dokin sunna tafe cikin nutsuwa ASADEEK ya sake tsayar da dokinsa ya kalli SHEIK ya ce" da ace zubewar nema ta yi da na san haka Allah ya hukunta ba rabona bace" SHEIK ya dube shi, a tausashe ya ce" Me ya samu madarar?" ASADEEK ya rintse ido, sai kuma ya bude ya dan kalli katon filin, da irin yadda wajen ya dauke sawaye tunda suka shigo, wa'inda ke tsaye du sun duka kawunnansu a kasa irin sunna masa gaisuwa da girmamawa ne A dan kufule ya ce" Yarinyar nan ta dauke, ta sha, ita da Auta" Da mamaki Sheikh ya ce" Yarinya?, Wace yarinya? Ko Hajia HUZNAH?" Baki ya tabe ya ce" HUZNAH ai nutsatsiya ce, baiwar Allah ce, wannan bakuwar dai mai kama da aljannu, itace ta dauka ko kadan bata rage min ba" Sosai SHEIK ya ji wani irin mamaki, hadi da dariya, bai san me yasa ba, abin ya dace ya bashi tsoro ko haushi? Aa shi dai dariya abin ya bashi, fuskarsa cike da yalwatacen farin ciki ya ce" Kwarai zan so na gaisheta Allah ya karra maka lafiya" Ido ya tsurawa SHEIK, sai kuma ya ce" Bata da hankali fa, wace gaisuwa zaka yi mata?, Da ta zo ce mana ta yi sasannunku fa, na yi lati ne dan na mance dan kwalina, latin awa daya ta yi ta zo mana ta dibe albarkar alkyabarta ta kallemu tsai tace sasanunmu fa akaramakalahu" A yanzu kam a dole ta fito dariyarsa, ya kai hannunsa yana tare bakinsa hadi da zarro ido , sai kuma ya sake waiwaigawa ya rage murya ainun ya ce" Kana tune a kulun idan Saraki na maka kirari , idan yace kai Zaki kake a dawa, a gidama zaki kake, sai nace uhum ko?, To yau ga amsarka, ina tsoron kaima ka shigo sahun maza masu sunnan maza masu iyali, a yanzu kake kokarin zama nama kiri kiri a gida, Allah ya karra maka lafiya" Gannin SHEIK ya mayar da abin na tsokana sai ya kada kai kawai ya ja Dokinsa ya nufi har kofar Fada ya sauko bayan Dogarai sun ririke dokin ana ta yi masa kirarin da aka saba Dubansa ya sake kaiwa kan SHEIK ya ce" Saraki bai yi karya ba, Me za'a nunawa HUZNAH ne?, Ni dama lalausar mace itace abin birgewata,..... SHEIK ka ji da kyau zaki nake har a kuryar daki" Dariya SHEIK ya saka sannan ta bi bayanshi suka shige domin ba zai tashi daga zaman fada ba yau sai azahar Shara'a ya gabatar ta wani mai gari, mutumen matansa hudu, yayansa arba'in da daya, matar tasa ta hudun ce da ya auro yarinya karama, domin sa'ar jikarsa ta goma sha hudu ce, ga yarinta, ga karamin jiki, abin dai ba'a cewa komai, ta samu kanta a cikin kishiyoyin da ba ruwansu da cewa yarinya take, aa kishiya ce sak, mutumen malami ne, ko nace malamin tsubu, a haka ya aure yar yarinyar iyayenta na zuwa amsar mata maganin iskokai dake damunta, aka wayi gari ta haukace shi take so Yar yarinya karama ta ringa tarda shi karshe dai mahaifinta ya daura masa fan gudun wata fitina ta bilo To fa tunda aka tare ne yarinya ta ringa tambayar me ta yi aka aura mata wannan mutumen? Shi kuwa ya yi iya yinsa ya karra daure mata baki, haka kuma tunda ta shigo a matsayin sabon abinci ya daina ziyartar kowace sai ita, karamin jiki yarinta ga abu ya girmameta sai rashin lafiya kala kala, tun ana daukan abin laulayi ne har aka gane cewa lafiya ce bata da ita kawai , kamar ana tsakurarta, fatarta ta dafe, komai dai sai handallah, tun mahaifinta na neman alfarmar a bashi ita ta kwana biyu a gida ta farfado sai a dawo da ita har abin ya fara tsoratar da shi, shi kam ita daya Allah ya bashi dan haka ya je ga yan sandan yankin ya sanar masu, ama babu yadda zasu yi da kai gari, domin da suka zo aka toshe masu baki, hakan ya saka shi neman hanyar da zai ga UMUGHLUK ITIBEL domin shine sarkin baban garin, domin kauyen na Agadaz ne Ya sha wahala ainun, domin sai da ya ringa haduwa da yan kasan shugaba masu lalata mulkin shugaba, wasu har kudi sun amsa a wajensa da nufin zasu masa hanya, abin dai ya gagara, a kadan ya dauki wata guda, gannin lamarin ya kasa samuwa ya je sallar juma'a a baban masalaci juma'ar da ta wuce Shi ya taya masu gyaran masalacin gyara da komai, yana nan masalacin ya cika har SHEIK ya karaso aka yi sallah aka gama Ana gamawa ya karasa ya bashi hannu ya fashe da kuka, domin lamarin na neman sakashi a halin ha'ula'i, matarsa kanta tana kwonce ba lafiyar sanadiyar wannan matsala, Allah ya taimakeshi ya fada kan SHEIK din, shine ya amshi numbarsa suka sake zaunawa ya sanar komai da komai Kwarai SHEIK ya ji haushin haka, har ya masa alkawarin sanar da ASADEEK, domin abu ne da ya shafi mai gari, ba su zasu yi shara'ar ba dole sai ASADEEK, Ya kuwa taki sa'a, da ya sanar masa menene sana'ar mai garin abin ya karra harzuka shi, Wannan zaman ne aka yi a yau, wanda ya kawo rikici sosai, rikici mai wiyar fade, ga dai yarinya a zaune ta fadi abinda take ciki ta kasa, haka kuma kishiyoyinta sun goyi bayan mijinsu sun fadi cewa tunda ta zo babu abinda akai mata , ita dai ta tsangwami kanta Abu ya so ya ja daga, domin su matayensa sunna tare da mijinsu da sarautar mijinsu, yarinya kuwa ta zama wata iri, wahala ta rikitata ta zama sai a hankali Sai da ya gama gane komai ya fara sauke masa rawanin , nan fa aka rikice, rawani a kasa sai hauka, abu ya cakule da kyar aka fadi gaskiyar sihirin da yake yiwa mata kafin ya aura, mulki na cin zali, babakere da kayan marayu, abubuwa dai babu dadi, sai da ya saketa aka wuce cel da shi dan yin bincike da fita hakkin masu haki a abinda ya rage masa, gunjin ihun da yake yi kan shi mai Aljani wane da wane za'a wulakanta kittt ya hadiye shi a lokacin da Murtala ya kafta masa mari a gabar haba da wuya har ya ji kamar fitar hakori a bakinsa, daga nan sai zanzana da kuka suka tafi da shi Basu tashi ba sai da suka saka ranar nada wani bayan dogon bincike, kafin nan aka wakilci limamin garin ya zama mai garin rikon kwarya bayan an samu shedar arziki a kansa A gajiye ainun ya koma bangarensa Ya samu ko'ina a kalkalce, a gyare yana fitar da kanshi Wanka ya yi ya sake shiryawa ya fice masallaci Bayan an gama sallah ya dawo ya koma dakinsa ya kwonta ba tare da ya nemi abinci ba, domin barci ke dan damunsa, dama ya raba dare yana aiki daga bisani ya yi nafila, kuma suka fita da sanyin safiya Lokacin sallar la'asar na gabatowa ya farka daga barcinsa ya sake shigewa bayi ya yi wanka ya kimtsa ya fice masalaci Yana dawowa ya zauna a falonsa na kasa yana duba wayoyinsa Tarin kiran da ya samu daga Bahija ya saka shi gyara zamansa ya yi kiranta Ba jan ajin nan ma, ba komai wayar na fara ringin ta daga tana mai sakar masa sansanyan kuka A yau kam ta kasa rike kanta cikin kukan ta ce" Haba bawan , Allah, me yasa zaka ringa wulakantani bayan ban cencenci wulakanci ba?" Zamansa ya gyara yana dan tausasa muryarsa dan son fara bin matakin da ya tsarawa kansa ya ce" Subahanalah, ki yi hakuri , bana wulakanci fa, Aure na yi kwanakin nan shi yasa bakya jina" Daga tsayen da take, sai da ta yanke jiki ta fadi, kukanta kuwa ya dauke cak ta yi wani irin zurru tamkar ta ga mutuwarta a gabanta A tausashe ya ce" Kina jina kuwa?" BAHIJA, bata taba sannin akoy wahalar da zata hannata kuka ba irin yau, wahalar da ta girmami kuka? Sam bata san akoyta a cikin duniya ba sai yau Muryata na rawa ta ce" Aure? Yanzu dan Allah aure ka tafi ka yi ni ina nan ina hauka? Wata ka je ka aura ni ina nan ?" Da yannayin mamakin furucinta ya ce" Ki yi hakuri, ban gane furucinki ba?, Kin san dama inada mata, sai na karra ta biyu ne" Ai kuwa, katon mikin da ya caki zuciyarta ita kadai ta san da zata ga matan nan nasa a yanzu ta yiwu da hannunta zata zama ajalinsu Da kyar take shalar iska ta bakinta tans dane kirjinta dan kar ya fashe mata Muryarta a cakule ta ce" Kana nufin, ka ce min, baka san ina sonka ba?, Ka san da har auren wani na kiya dan ina jiran na ji dagaa gareka?, Ni ina sonka, kuma ka san in ba so ba, ba zan zauna gadinka ba ko?" Shiru ya yi, har sai da ta dago wayar a tsorace tana kallo dan tsoron kar aje ko ya kashe din da ya saba ne? Gannin da haske ta sauke ajiyar zuciya ta sake karawa a kunnenta tana fadin" Hello? Dan Allah ka amsa ni" "Kina so na?, Kika kasa fada min?, Ai ba laifi bane fadin abinda yake zuciya, bale ina girmama soyaya ni" ya fada a sanyaye, yana sake sauraronta Sosai Bahija ta ji wani sanyi sanyi na ratsa mata zuciyarta A hankali ta ce" Na so na kwatanta, tsoro ya hanna ni, kanada mugun kwarjinin da na jima ban hangi dan Adam da shi ba, da na san zaka dubeni da na kwatanta" Bakinsa ya dan tabe, sai kuma ya dan murza goshinsa yaa ce" Kika ce, auren wani kika kiya?, Kar dai ki ce min iyayenki kika bijirewa a kan gaibu?" Bahija ta yi tsuru tsuru, jin amon muryarsa a nan ta tabata idan har hakaan ne yana iya yin fushi, kai tsaye ta ce" Aa, ba bijire masu na yi ba, su suka bada BAIWATA a kambacina" Dukkan da maganar ta yi masa sai da ya ajiye wayar a kasa ya zuba mata ido yana kallonta Afkawa da ya yi a tunani ya saka shi manta waya yake yi har ta kashe a rikice ta sake kiransa kusan sau hudu sannan ya mika hannunsa ya dauko yana sake kallon sunnan ya daga ya sake kusantata da kunnensa ya yi shiru *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣6️⃣ Ya daga ya sake kusantata da kunnensa ya yi shiru yana sauraro "Dan Allah ka saurareni, bana so ka yanken hukunci kai tsaye, ka sani ni ban taba soyaya ba, ban taba sannin yaya take ba sai a kanka, iyayenaa kuwa ba bijire masu na yi ba, kuma mijin da suka so bani ba sonshi nake yi, na tabata shima haka, ka ga hakan bashida wani anfani ko?" Ta fada muryarta na nuna tashin hankalin da take ciki A hankali ya iya bude bakinsa, ya ce" Baiwa?, Baiwarki?" Tambayar ta zo mata a wata iri, dan haka ta nemi karrin haske A tausashe ya ce" Kina nufin ke din jinnin sarauta ce?" Amsar da Bahija ke tunanin a gaban kowa tana iya badata da takama da isa domin abu ne na isar da takamar kasancewarta yar sarki, a yau sai ta samu kanta da mugun tsoro da zulumi, bata san me zata ce a matsayin amsa ba, tana tsoron ta fadi abinda ya saba muradin Balarabenta ya bace mata kamar yadda ya saba, hakan ya saka ta cewa" Baka son famillyn sarauta ne?" "Kusan haka, kin san ni lamarin sarauta ne bana so, bale auren yar sarakuna? Anya zata iya yin biyaya? Gashi inada aiyukan da basa son ciwon kan mace!" Ya fada yana sake danne zafin da kirjinsa ke yi masa Muryarta ta tausasa sosai, a sanyaye ta ce" Sarautar ba wata mai karfi bace, idanma da hali mu bar maganarta , ka dauka ni ba jinnin sarauta bace in dai hakan ne zai faranta maka, dan Allah ka zo gidanmu, ko ni ka fada min a wace kasa kake da gidanka, zan zo, zam zo walahi" Da kyar ya sake iya bambarar bakinsa ya ce" In sha Allah, zan saka rana na zo, zan yi kiranki domin bani da isashen lokaci" Haka yauma, tans ji tana gani, bata koshi da sauraronsa ba, bata san matsayarsu ba, bata gane zai zo din ba da gaske ko aa?, Ya katse kiran da nufin yana busy, haka kuma ta damu kanta da sanyaya zuciyarta, da fadawa kanta cewa ai da sauki, wanda zai tashi ya taka leda, ko ba komai sannu sannu bata hanna zuwa, ta tabata a yanzu da ya ji saboda shi har ta ki auren wani zai dubeta, ta tabata kuma zai aureta idan suka zauna, in har maganar sarauta ce baya so ba sai ta fada gaskiyar asalim sarautar tasu ta yayane suka sameta ba?, Tunda abin na neman hadawa da farin cikinta komai na iya faruwa, ciki harda iyayenta walahi! (To dai, baki ke yanka wuya) .................................................... *BAIWA?* Baiwarta? Wace irin baiwa? Baiwa dai? To ama, shi kansa ya shiga cikin duhu Bawa fa du yancin da zai samu kansa kasa yake gaisar da uban gidansa Babu mutumen da ya san darajar sarki da tsoron sarki irin bawa Bawa komai fitsararsa fa son duniyarsa a tsorace yake da sarki Du arzikin da bawa zai yi a duniya kuwa idan ya tashi gaishe da sarki sai ya duka Wacece ita a duniyar bayi? Wace irin wayewa ce da ita a lamarin bayi? Ta yaya zata kasance Baiwa bayan idannuwansa take kallo ta ki bashi amsa? Ta yaya zata zamto baiwa, bayan ta yi sa in sa da Huznah? Wacece ita a duniyar bayi? Su waye iyayenta a tarihin bayi? A hankali ya sake gyara zamansa Afkawa ya yi a tunanin me yasa za'a aura masa baiwa to? Yaya sunnanta na gaske? Me ta zo yi? Shin Umma ta sani ko bata sani ba? Tabas wani abu ya dan tsaye masa a rai na hargagin da Umma ta yiwa yarinyar nan a jiya, Koda karama ce, koda Umma uwa ce a wajensa, Yarinyar sarauniyarta take, a laluma ya dace ta dakatar da ita .......ama, ama sai......... Da sauri ya kore wannan tunanin yana astagfari, domin ya gane shedan ya fara kawowa tunaninsa hari Wayarsa baba ya dauka ya yi kiran number Umma A tausashe ya sanar mata a sanarwa HUZNAH da Auta yau ba zai yi zama da su ba a falo Ta tambsyeshi tana fata lafiya yake? Harda nuna masa cewa zaman da yake yi da auta tana jin dadinsa domin Auta na kwontar da hankalinta idan tana tare da shi Ya tabatar mata lafiya kalau, yana da bukatar hutu ne A dole ta hakura ta yanke kiran Wayar tafi da gidanka ya janyo da kansa ya sake zaunawa yana dan tunani A nutse ya bude litafi ya saka code din bangarenta A irin wannan lokacin zaune suke sunna hira da kyakyata dariya ita da Innarta, Kukan shigowar kiran sai da ya saka suka tsorata sannan suka zubawa abinda ke ihun ido Da kyar a kira na biyu Innarta ta yi shahada ta karasa tana fadin" Ki tsaya ke dai daga nesa, idan kiran mai sama ne ya sameni kya fadi ga abinda ya kasheni, ama ni kamar ma gani a wayar Habu wani lokaci muna kallon masu jan kunne kamar salula ce, bara dai na gani" NADIRAH ta yi tsuru tsuru, ita dai ta ga abin nan har a dakinta, har a kicin dinta, ko'ina fa, tace kwaliya sai yan birni, sai ga abu na kuka kirrrr kamar tsohon keke mai rubabiyar kaca?, Allaaj jishe su alkhairi Takarkarewa Inna ta yi tana dagawa ta ce" Hallo, Hindu ce a kan layi waye ke magana?" Shirun da ya biyo baya ya saka Hindu cirewa ta kalli NADIRAH ta ce" Indi anya waya ce? Kin ji shiru kamar mutuwa ta gitta" Karasowa ta yi, da sanyayar muryarta wace idna ta yi magana da ita kamar ba zata tofa komai ba sai zikiri ta amsa gana fadim" Innata bara na ji, Mutun ko aljan daga ciki muna sauraro" Gaban goshinsa ya sake dafewa a hankali yana shafawa yana tunani a zuciyarsa A hankali ya furta" Da dare, ina son ganninki a Bangarena" Wata zabura da ta yi ta fancakalar da abin wayar a zabure, kasa kasa sosai ta ce" Inna Abanku ne Fa" saurarawa ya yi sosai yana jin abinda suke fada, Abansu? Aban su wace inna toh? Innarta kuwa sai da ta wuntsila tana dora hannayenta a kai ta ce" Kin ga NADIRAH zan ci ubanki Habu bilahilazi, yaya zaki ce Zaki ne ya kira?, Ta yayama zaki zai kira?, Bayan wannan ina yan aike da takarda? Ke kam inaga dole na fara neman na aljanu kuma, abin na rikecewa a hankali bamu gane ba" NADIRAH ta dauki abin ta mayar ta makala ta zauna kusa da Innarta ta ce" Innata walahi muryarsa ce, abinda na san muryarsa yadda kika san rusheshen kato idan yana magana, bobobobobo abu a hade dai kin gane ba kamar maganar Aminu aminu ruwan sanyi ba, jiyan nan ma fa ya ja min kashedi, cewa ya yi da dare na je, na je na yi me kuma? Ni mai kaurin sunnan nan,ban yi bama ance na yi?" Da kyar innarta ta yarda, sai kuma ta shiga yi mata nasiha tana cewa ta yiwu wani abin ne , sannan ta shiga tsoratar da ita da kiyayewa da yi masa haye, sannan ta kyaleta ta mike ta shiga tunanin me ya dace yau yar ta saka? Lamarin ne kowa na kula nasa a boye, itama tana tura NADIRAH da su kwaliya su gyara jiki su matsewa a zuwan ta saka abinta ta more, kayanta ne, kuma ba haramun bane kafin su tafiyarsu ta san ta mora, ita kuwa gaba gadi ta yarda. A bangarensa kuwa sunnayen nan uku uku ya kawo ya hade da maganar da ya yi da BAHIJA Kai ya girgiza yana dan tunani, sai kuma ya mike a nutse ya haura sama domin ya hanna kowa shigowa dan hidimta masa wani abin idan ba shi ya bukaci hakan ba ____________________________________ Zuma ce farar saka, irin sabuwar nan mai kyan gaske Hindu ta juye a cikin hadin da ta yi na gumbar mata ta dameta sosai sannan ta rufe a kwano mai kyau ta sake nufar dakin INDI Kwonce take a kasa, watau saman kafet barci na wartarta, jikinta wando ne irin mai laushin nan mai lafewa a fatar jiki , sai riga mai siririn hannu wace ta dauke mula mulan mamanta , domin mamanta ba yan biri biri bane gaskiya, ta baje tana barcinta hankali kwonce HINDU ta zauna tana tashinta a hankali Dagowa ta yi tana shanye lumsasun idannuwanta ta ce" Inna barci fa nake zaki tasheni?" HINDU ta ce" Na sani, ki tashi ki je ki ji kiran da yake maki mana" Baki ta turo ta ce" Inna, na fara barcin? Ki bari sai gobe mana" Kai ta girgiza tana talabota ta ce" Kin ga damu na yi ungo shanye ba yawa, kuma ki je ki dawo ki yi kwonciyarki, kin dai ji abinda Aunty tace ko?" Sosai ta sake bata fuska ta amshi abin sai turo baki tale yi ta dan kafa a bakinta Dandanon zakin ya sakata bude bakin da kyau ta shanye sannan ta nemi neman komawa ta kwonta, bata san abinda ta shawa kanta ba, Gumba ce VIP, gumba ce ta gagararum matan da suka san kansu suka kuma yarda da kansu, a hadin gumbar ana saka sinadarai na mugun motsa sha'awa, ko budurwa kike idan kika sha sai lamari ya motsa maki bale wace ta san hanya, gumba ce mai saka ka tamkar ka yi maye, karfi ne da ita dan idan baka saba shaye shayen magungunna bama sai ta bugaka, gumbar tana gagawar tara maka ruwa a mara ne ka ji har kana juwa Da sauri Innarta ta mikar da ita tana shafa mata ruwa masu sanyi a fuskarta tace" Tashi mana ko sai na kwada maki mari?" Kamar zata fashe da kuka ta ce" Allah ba zan yi wanka ba, a haka zan tafi, bani malun malun din na rufa , kuma ni idan suka ce zasu ci zalina Allah sai dai kowa ya kwaci kansa dan ba zan yarda ba" Ita dai HINDU bata ki ba, asalima turarukan da ta siya a wajen Nana mai kayan mata ta bude du ta shafe yar da su, sannan ta rufa mata alkyabar ta kuma dauko turare ta yi mata wani wankan da shi sannan ta saka hijabinta ta ce" Mu je na fan taka maki, kin ji yar albarka?" Ba dan ranta ya so ba ta tafi, a yau tana zuwa da harare ta zoma Dogaran, sai dai ga mamakinta basu dakatar da ita ba suka barta ta shige Allah barci take ji, dare ya yi fa, hakan ya sa tana shiga wajen lalausar kujerar dake hakimce ta nufa tana bake alkyabarta ta yar a nan ta haye ta yi daidaiya ta shiga barcinta mai dadin balaki, barci kamar an aiko mata shi, barci mai mugun dadi Madarar da ta yi saura a kofin ya idasa shanyewa ya mike daga saman table din a ransa yana ayyana ' Ya isa haka kuma, ba zan iya rayuwar shiririta ba, har nine zan ce yarinyar nan ta zo ama dan raini bata zo ba?, In sha Allah gobe karfe takwas zan tara kowa a gidan nan na bayana masu na gane wacece ita, a bani bayanin abinda yake faruwa sannan na sawake mata, bana son shiririta, in bandana rashin girmama baba shi bai girmeta bane? Tafiyar yake yi yana warware rawanin dake kansa, domin so yake yau ya kwonta da wuri, tsakar dare sai ya tashi ya yi nafila bi'izinillah Ya idasa warware dogon rawaninsa na turkudi yana dan tatareshi a hannunsa idannuwansa suka sauka a kanta Yannayin kwonciyarta ta watsa ƙafafuwan ne, ta yi ruf da ciki ta soka hannunta ta kasan cikinta ta kaishi inda sam bai gane ba, cikinta ne, ko cikin wandonta ne Gashin kanta kuwa a barbaje yake a jikinta da saman kujerar, barci take yi haikan A hankali ya kifta idannuwansa yana sake kallonta, sai kuma ya kalli Alkyabarta dake yashe a kasa, Rawaninsa ya dan yafa a saman kansa ya shiga takawa dan zuwa inda take Wajen alkyabar ya ja ya tsaya, ya duka ya dauke a hankali ya karasa ya ratayeta sannan ya karra juyowa ya zuba mata ido Tabas bata shafi jinnin sarauta ba, domin jinnin sarauta baya yarda Alkyaba a kasa koda ta tsufa Gaban goshinsa ya dafe yana rintse idannuwansa Bai taba haduwa da abu mai buga masa zuciya ba irin na yau Sarkakiyar abin na damunsa Yana son sannin amsoshin tambayoyinsa Yana wannan tunanin ya karaso , a saman kujerarsa ne ta baje take barci, kujerar da ko Umma bata hawa, Auta cema kan hau idan ciwonta ya tashi tana kuka ta rukunkume shi idan yace ta bi Umma, bayanta ko Huznah sai dai ta duka a kusa da kafarsa bata hawan masa kujera sam A hankali ya zauna a kusa da kafarta ya saka hannunsa yana buga gefenta, watau saman kujerar da dan karfi yana fadin" Ke, Ke tashi!" Da kuka kukan shagwaba ta dago gaba dayanta idannuwanta na rufewa tana budesu da kyar, kaffafuwanta na rawa, jikinta na amsawa, kawunnan mamanta na yi mata wani irin zogi, uwa uba Mararta tamkar zata tsinke, hannunta rabi a cikin wandon ne rabi kuwa a saman mararta ne, hasalima ba cikin wandon ta aika hannun ba gaskiya, mararta take dannawa dan ta samu sasaucin azabar da take ji, Bata bude idannuwan nata gaba daya ba ta fashe da kukan Tabara ta ce" Wayo Allahna Inna nonona ciwo, inna cikina ciwo, inna duwawuna na min ciwo kamar zasu cire innata" "Innalilahi wa inna ilaihi rajune............ Hasbunnalah, Hasbunnalah Hasbunnalah................ " Da sauri yake fadi har yana kamo wani da wani sannan ya nemi zubewa kasa domin NADIRA rigar tata ta dage tana nunawa Innarta wajen dake ciwon........................................ Jama'a mu taya shi salati😭😭😭😭😭, yanzu yar nan kim dage sai kin kashe mana Zaki? Iyi? Me muka maki ne? Haba yar gidan Habu makadi😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ Happy juma'a yan uwana musulmai😍 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣7️⃣ Da kyar ya iya tsayar da furucin bakinsa ta hanyar ambaton sunnayen Allah, sannan ya iya cire dubansa a kanta ya yi kokarin mikewa domin gaba daya rigar ta kama ta cire ta yar tana ihun nononta Wata irin sarawa kansa ke yi, da karfi da yaji yake cire dubansa sai kuma ya samu idannuwansa da komawa su manu a kan haannunta dake murzar kan tana doka kafafuwanta tana kukan nan ciwo, nan ciwo Bai gaba gane ya shiga uku ba sai da NADIRAH ta silalo kafafuwanta kasa ta ja wandon dake jikinta ta cire kafa daya tana son sabule dayar ya damke hannunta da wandon, idannuwansa na sake kadewa sunna sake yin ja, hannayensa na sake bayanar da birdin tashin hankali, yannayinsa na sake rikidewa ya kamo dayyar kafar tata da karfi ya zira a wandon ya mikar da ita kirjinsa na wani irin mumunan dokawa ya nemi jan wandon sama Sai dai kashhh, shi yake kokarin mayar mata, a lokacin ne ta fada jikinsa ta yi masa wata irin rukunkumewa tana mai fashewa da kuka, abin ya girmami tunanunta, kamar ana mata tafiyar tsutsa a sansan jiki, gana daya ba a cikin hayacinta take ba, wannan gumba itace gumbar jaraba, ta yiwu harda maganin nasara na karrin karfin sha'awa a cikinta, idannuwanta sun rufe, abinda take ji take so ta daina ji, bakinta sunnan Innarta yake kira da fada mata wajajen dake mata zogi da irin yadda take ji A rikice ya sake kokarin bambareta daga jikinsa yana neman fita a hayacinsa, wannan wani irin tashin hankali ne? Shi kam yanaga wannan itace jarabawarsa toh ba rashin zamowa namiji ba, kafin kace menene wannaan jikinsa ya yi wani irin mikewa da mahaukacin amsawa, Hannayensa rawa zuke yi, goshinsa na fitar da zufa Tareta yake yi, ita kuma hannunsa take rikewa da yake taretan tana jimkawa a saman maman nata tana sake shigewa kirjinsa Bai ankara ba gaba daya kafafuwanta suka gaza daukarta ta yi baya ta kusan tikuwa a kasa, jikinta ya kara saki, ya zamto yanzu ciwon da take ji ya gama yi mata riko mai tsananin gaske, bata san menene bama bale ta san hanyar magance shi, ta gama ji a cen kasam zuciyarta cewa yau ne karshenta ita kam, shikenan karshenta ne ya zo, zata koma ga ubaangijinta a haka? A hankali yaa iya tarota, rufar dake kansa ta zame ta fadi kasa Bai kula da dauka ba ya cicibota ya talabota a jikinsa yana kallon yannayinta, yadda jikinta ya saki din nan stlll hannunta a saman kirjinta sai ya ji zuciyarsa na yi masa zafi Zafi ne yake ji mai tsananin gaske Haka kuma irin yadda yake jin jikinsa bai taba jin haka ba, tunda yake bai taba kallon abinda ya gigitashi haka ba, tsakaninsa da HUZNAH bata taba magana ta rashin kunya da taba jikinta haka a gabansa ba, shi yasa lamarin ya zo masa bako, ya ji wani irin abu mai karfin gaske tamkar ice a jikin nasa A hankali ya idasa dorata a kafadarsa sannan ya kama abin matatakalar ya shiga haurawa da ita, kirjinta ba komai, wandonma ta sabule shi sai dan pant din dake ciki fari kal, hakan ya hadasa masu da contact body direct, duda da riga shi a jikinsa, ama bai hanna jikinta gogar wasu sashe nasa ba Da kyar ya iya laluben kofar ya shiga da ita ya karasa saman tafkeken gadonsa ya shinfideta sannan ya zauna a kasa ya tataro kafafuwansa ya harde hannayensa ya saka kansa a ciki yana jin inama zai iya fashewa da kuka mai tsanani? Da ya yi dan ya ji saukin ciwon dake damunsa Ta yiwu ta saba harkarta da maza, domin alamun da take nunawa so take yi a yi mata, shi kuma gashi bashida wannan ikon, sai dai ya mike ama bai isa ya yi ba Sai dai a yau yana tunanin zai iya saka abin nan aa bakinta ko zai smu sasauci, domin idan bai yi ba azabar zata yi masa yawa, yana iya kashe kansa a banza, idan ya so in ya rabu da ita sai ya ci gaba da zamansaa da matar rufin asirinsa Muryarta a jigace ta sake nade jikinta tana fashewa da wani sabon kuka, domin abinda ya yi mata uwa dutsi a Mara ne ya sake murda mata Jajayen idannuwansa ya bude da kyar ya mike yana hayewa saman gadon ya saka haannayensa ya janyota gaba dayanta jikinsa yana gyara nadewar da ta yi A hankali ya zubawa fuskarta ido da ta yi jajajir har ta yi kamar ta dan kumbura Kallon fuskar yake yi a ransa yana ayanna magana kamar haka' Ban san takamaiman wacece ke ba, ban san me kika zo rayuwata yi ba, hasalima an taabatar min ne kawai an dauran aure da ke, bayanshi ban san komai ba, ta yiwu idan naa taba ki zan mutu, ko wani abin zai sameni?, Ba zaan daina tabaki ba domin a yanzu na fi yarda da idan ban taba ki bane kamar wani mugun abu zai sameni, na yi imani da Allah, na kuma yarda da bawa nake ko mecece ke ban isa na karewa kaina ba, sai dai Allah ya kare min......., Zan ribanci albarkar jikinki koda hakan shine sanadiyar barina duniya......' Yana kai karshe ya saka hannunsa ya janye nata hannun dake rike da mamanta ya maye gurbin wajen da hannunsa a hankali ya shiga masajin maman da ya ji su basu da laushin nan lugub lugub kamar yau aka fara matsa su, Jin dadin tabasu yaske har cikin ransa, hakan ya saka shi kai bakinsa ya shiga basu kulawar da ta dace dan kara sakankancewarsa ko zai samu shima ya rabu da nauyin dake jikinsa Mika ta shiga yi, a hankali tana ji du idan ya dora bakinsa a waje zogin nan na bari, harma ta ringa jin wani kaikayin dadi kamar yyana sosa mata, hakan ya saka a yanzu rikoshi take yi har tana shafa gashin kansa dake saman kirjinta tana sake sakin jikinta dan wani iri kamar abu na kuncewa a mararta ta fara ji A hankali ya ringa bin du inda ya dace ace ya bi da ita, irin yadda take amsarsa tana sauke ajiyar zuciya ke karra masa kaimi , kamshin jikinta, da tsaftar jikinta kuwa ita ta fi komai karra jansa kamar gam a jikinta haka ya zama, laushin jikinta, santsin fatarta kuwa ba'a cewa komai, zumudi zai kirayi abin na sabon lamari? Ko kagara ya fitar da jarabar dake kara saka masa zafin mara? Shi dai komai nata zai kireshi da perfect a wannan gabar Sam bai yi gigin janye oant dinta ba, hasalima nasa ya janye gaba daya ya cire komai , dama ba fitila ya kunna ba, ta bayi dake kunne ce ta dan haska dakin, kai koda fitilar a kunne karamin abu ake tunawa ba wannan ba Dukkan abindayake gannin ya dace ya yi mataa ne yake yi mata, kuma kwarai ya ga ikon Allah a pant dinta, ama kuma sam bata da alamu ta saku bale har ta gane abunda yake faruwa da ita hannunta ya kamo a lokacin da ya karasa kusa da bakinta a hankali ya shiga kissing din bakinta sannan ya dora hannunta a lamarinsa ya jimkaa ko zai samu abinda yake so, duda hannun nata ya yiwa abin kadan, ama haka ya rike sosai yana ta so ya samu kansa Tun yana tunanin yana iya kawowa har ya fara sarewa, sam ya gaza kawowar gashi kana kallonta zaka gane ta fa fara jigata da jijigar nan A jigace ya sauka daga jikinta ya koma gefe ya yi reran yana kallon sama Idannuwansa sam basu da dadin kallo a irin wannan yannayin A hankali yake kiran sunnan Allah a bayane, sai kuma ya rintse idannuwansa yana adu'ar Allah ya raba shi da wannan ciwon Ciwo ne mai tsananin gaske wanda sai shi da yake rayuwa cikinsa ya san zafinsa Ciwo ne mai saka shi jinsa shi ba kowa ba, ba komai ba, Idan ya samu mikewar lamarinsa yanna jinsa wani kakarfan mutun, mutun mai daraja A lokacin da abin ya kwonta lagwab sai ya ji du duniya banzama ta fi shi a idannuwan macen da ya dace ace shine Hero dinta Haka kawai ya ji bama zai yarda ya ji irin wannan sensation na humiliation din ba a gaban yarinyar nan, sai dai zuciyarsa tai masa nauyi Ga mace fa, mace har mace, sai dai ba damar ya bata abinda namiji ke ba mace, me ya kai wannan karyar da zuciya? Dumin fatarta da ya ji a gefen cikinsa ya saka shi rintse idannuwansa da suke bude yana kallon sama Sukur sukurtu da take yi dan mararta ba wani sakuwa ta yi ba ya saka shi dan matsawa kadan yana sake rintse idannuwansa, kai yau ya ga tashin hankali da yarinyar nan, wai ba zata barshi ya dan yi jinyar zuciyar tasa bama? Hannunta ta sake kawowa dan ta kuma damkar mararta, ta haka ta sakkar masa dukan da ya saka shi bude idannuwansa da sukai masa nauyi a karkato da dubansa gaba daya ya zuba mata ido a hankali ya ce" Me kike so?" Shi ya yi maganar, kuma shi ya ba kansa amsa Sake zuba mata ido ya yi, ta firgice, ta rikice, ama a haka bai taba gannin halita mai laushin kallo a ido irinta ba, bai san dalili ba A hankali ya sake yi mata runfa , ba dan zai iya cire mata damuwarta ba, sai dan ji da ya yi a ransa kamar yana iya kai harshensa wajen da zai iya sama mata nutsuwa Bai san baban tashin hankalinsa ya tono ba a lokacin da ya cire dan kankannin abinda ya rage mata a jiki Duhu duhun dakin bai hannashi bin abinda ke jikin pant din da ido ba A yanzu kam ba hannayensa kadai ke rawa ba, gaba daya jikinsa ne ya kwashi rawar har ya manta da humiliation din da yake samun kansa a ciki idan ya kasa tabuka komai ya wara kafafuwanta yadda yake gannin ya dace da bukatarsa a rikice bai ko yi addu'ar saduwa da iyali ba, domin tun a farkon romancing yake yi, ba dan komai ba sai dan ya tsaftace taba iyalinsa, ya san iyakarsa nan, bai sabawa kansa yi idan ya zo zuwa baban birni ba Cinyoyinta kataba kataba ya rike, yana sake kallonta a birkice ya kawo jikinsa zuciyarsa na babalewa , yana tare da tsoron kwashe abinsa kamar tsuma ya auna kansa yana mai rintse idannuwansa Zaburaran ihun da ya ji an ce wasu matan na saki na wahala idan aka ratsa tantanin budurcinsu ne ta saki, wanda bai taba tunanin zai ji a kunnayensa ba, hakan ya saka masa tsoro da firgici ya dago a gigice yana kallonta fa kuma kallon jikinta Eh haka ne, shine ya samu isa wannan duniya, dumin duniyar ne ya samu sauka a jikinsa A rikice ya sake riketa fan son kubcewar da take yi tana bude idannuwanta tarrr tana saukewa a saman fuskarsa da sake dagowa a haukace ta saki kuka tana rarumar fatar jikinsa tana kaima yago dan ya saketa ya barta da azabar nan da ta farkar da ita daga wata azabar A hankali ya kwonta a jikinta, da dan karfi ya hannata motsi ya kai bakinsa wajen kunnenta, muryarsa bata fita da kyau, karshema dumi dumin abinda bai san yana fita a idannuwansa ba ke diga a kumatunta, karshe sai a zuciyarsa ya iya kamala adu'ar sannan ya shiga gwada abinda a kulun sai dai ya yi a mafarki, Innalilahi wa inna ilaihi rajune, ya Allah, ya Allah, ya Allah, baban rikicewa kam ya samu kansa a ciki Du yadda yake tunanin abin ya wuce da tunaninsa, karfinsa ko dabararsa Allah ne ya halatawa bayinsa wannan ni'ima, ya basu damar ziyarta a duk lokacin da suke so Allah ne ya basu wannan dama da malakar wannan lamari Ya jima da gonar a gefensa ama bai taba shiga ba Yau, lokaci daya, gona ta yi yabanya ta yi kyau, bai zaci zai anfana da albarkatun cikinta ba sai gashi tsamo tsamo a ciki? Dole ya wawuri nan, ya cafki cen, dole ya ci itatuwar da ta dace da wace bata dace ba Tun yana gane kansa har ya saki kansa Tun yana jin wahalar wajen da matsewar wajen har ya saba Baiwar Allah a matse take tam, ama a haka aka mata huji zuwa daya, sannan aka shiga sabar da ita da kayan manya Wahala ta sha, tana kan sha, domin bata san lokacin da numfashinta ya bar gangar jikinta ba, ta summe gaba daya, domin a zuwan farko da ya yi mata wata wawuyar damka du ta san me ake yi, a zuwa na biyu ne karfinsa ya ninka na da, yake hakarta tamkar ba gobe, da kyar ya iya sarara mata ba dan baya son kai safe a kanta ba, sai dan a yanzu ne hankalinsa ya dawo jikinsa har gane halin da suke ciki Jikinsa ba karfi ya konta a gefe, jikinsa da mugun zafin zazabin da ya karyo masa ya mika hannu wajen da ake ajiye masa ruwa ya dauko jug din a hankali ya bude ya shiga diba yana shafa mata kadan kadan a fuskarta Wani irin numfashi ta ja, watau ta dawo daga duniyar summar, ama kuma idannuwanta a kule ruf Idannuwansa ya rintse bayan ya ajiye a hankali ya sake daidaitawa ya dagota ya dorata gaba dayanta a jikinsa sannan da kafarsa ya janyo abin rufa ya rufa masu A irin wannan lokacin da ace zata iya daga dan yatsarta, da ta daga ta aikata aiki irin na mahaukaciya Sai dai azabar da take ji, ita bata gane komai Wannan mutun da fuskarsa ke cikin idannuwanta bata sanshi bama, azabar da take ji ta tsayar da tunaninta waje daya, Radadi, zogi kuwa ji take yi ko numfashin nan da take saukewa idan har ta yi da karfi to fa lalle zata iya idasa hade gabanta da bayanta ne Lahaula wala kuwata ila bilah Innalilahi wa inna ilaihi rajune Wayo Allah Wayo Allah Wayo Allah Menene wannan? Wace rayuwa ce ita kuma wannan? Me ta gani a yau? Me ta rayu a cikinsa a yau? a cen kasan zuciyarta, sunnan mutun daya take ihun kira, watau *INNNNMNNNNNNNNNNNNNNNNAAAAAAAAA* Barci mai nauyi ne ya dauke shi, irin barcin da a tarihin rayuwarsa bai taba yi ba, kila ko da yana jariri, ama a yanzu kam, barci ne da ya gagari idannuwansa da dadewa Irin motsin da ya yi a tunaninsa motsawa ce ta farko ta tsakiyar dare ya bude idannuwansa ya ji hannayensa sun wani urin sagewa sakamakon irin kwoncin da ya yi da rikon da ya yi mata da hannayensa biyu duka a kirjinsa ya saka shi dan sasautawa yana sauke idannuwansa a saman gashin kanta mai yalwar baki da cika A hankali ya juya wajen agogo Abinda ya gani ya saka shi tunanin yaushe agogon dakinsa ta lalace? Juyar da kansa ya yi wajen taga, duda a rufe ruf ama ya zuba idannuwansa Kyalin ranar da ya gani ya saka shi zarro ido a bayane ya furta" Subahanalah" Da sauri ya dago da ita a jikinsa, hakan ya sakata sakin dan karra tana sake rintse idannuwanta kam Fuskarta yake dan kallo, sai kuma ya yaye abin rufar gaba daya ya nufi bayi da ita Shi bai san abinda ake yiwa amaryar da ta kawo mutuncinta ba gaskiya, ama duda haka sai ya so tsayar da ita kasan pampo dan ya taimaka mata ta yi wanka Yanzu kam cizon da ta dirtsa masa a kirjinsa ya saka shi sakin dan kara yana dago fuskarta ya zuba mata ido Wani mahaukacin harara da take zabga masa ya saka shi kikifta ido yana kallon fuskarta ya ce" Kai me na maki?" Wani hararen take karra zabga masa mai tafe da sakon zuciyarta sannan ta rike abin shower din da hannunta ta masa nuni da ya bata waje Ido ya zarro yana kallonta, sai dai yadda gaba daya jikinta ya dauki ja bama iya fuskarta ba da irin fushin da yake gannina fuskarta ya isa ya saka shi bin umarninta Da baya da baya ya ja Tawul ya daura a iya kugunsa sannan ya fice ya nufi waje ya nufi bayi da sauri dan sallah itace yake so ya fara gabatarwa kafin komai, duda ya san me shirunsa yake nufi a waje , ama ya fi so sai ya yi sai ya fuskanci sauran 🙄🙄🙄🙄 Kai ku fa hawayeni🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣8️⃣ A dan hanzarce ya yi wanka hadi da wankan tsarki da ruwan dumi sannan ya fito ya koma dakin nasa Cikin gagawa ya saka kayan sallah sannan ya karasa kilatatacen wajen da yake gabatar da sallarsa ya shinfida dardumar dake kilace ya hau ya tayar da sallah cike da jin kunyar gabatar da sallar asubah karfe takwas da wani abu Yana gama sallah ya dukar da kansa yana addu'a, Gaba daya ya rasa wace irin farin ciki yake ciki a yau, farin cikinsa ya girmami tunanin bawa, wai shine mara a sake , shine yau magidanci? Ya Allah A hankali ya mike bayan ya gama yiwa Allah godiya sannan ya koma hanyar bayin yana tattare hannun rigarsa Da mamaki yake kallonta, ta hade jikinta da shower din ruwa na zuba a jikinta Da dan hanzari ya karasa yana dan bin ruwan da kallo kamar wanda ke dan sauka ta cinyarta da dan jini jini A hankali ya saka hannunsa a daidai bayanta ya tabata da nufin juyo da ita, Tsorata ta yi, ta juyo da dan sauri dan bata ji shigowarsa ba Rai bace ta saka hannunta ta doke nasa tana kara matsawa jikin garu a hankali kamar zata saka ihu dan azaba Zuba mata ido ya yi yana karantar fushinta, wannan fushi nata anya na tana jin ciwo ne kuwa? Wannan fushi nata kamar na ya tabata ne? Kara matsa hannunsa ya yi dan gaskatawa, ai kuwa ta sake doke hannun nasa tana rintse idannuwanta, hakan ya saka shi yin baya kadan yana zuba mata ido Rasa abinda zai ce mata ya saka shi juyawa ya sake ficewa ya karasa wajen wayoyinsa ya dauki daya ya zauna yana dubawa Tarin kiran dake wayarsa ya shaidaa masa tabas da jama'a a kofar dakinsa, watau cen kasa ana jira a ji ko lafiya Bai taba rasa sallar asubahi ba, in dai ba tafiya ya yi ba, jinshi shiru zai saka mutane a damuwa da tunanin ko lafiya? , Ciki harda su Umma fa Auta fa Huznah A hankali ya dannan number SHEIK Ko ringin din kirki bata yi ba Sheikh ya daga yana yin salama hadi da fadin" Allaj ya taimakeka, me yake faruwa? Kana ina? Lafiyarka kuwa?" Idannuwansa ya lumshe a hankali ya furta" Alhamdulilah, ka shedawa kowa Alhamdulilah" Ajiyar zuciya Sheikh ya sauke yana ji yana fadin cewa alhamdulilah, UMUGHLUK ITIBEL ne a waya Umma dake tsaye ce ta fara bukatar a bata wayar, ama sai Sheikh ya ce yana zuwa domin ya ji kamar ASADEEK din bai gama magana ba ASADEEK dai da kyar ya iya samun bakinsa da sake fadin" Ban san ba, ko Umma za'a sanarwa, ko kuma yaya ake yi dan taimakawa, gaba dayama bata so na tabbata" Shiru ne ya biyo baya Gaban Sheik ya ringa dokawa da sauri da sauri Cikin dabara ya juya ya yi nesa kadan da mutane, sannan ya sake juyowa ya hangi HUZNAH da bayunta a tsaye, babu wanda zai shiga ne dan bai bada dama ba, kuma adadin lokacin da ake dibar masu dan gannin ko lafiya bai cika ba bale su shiga Muryarsa a sanyaye ya ce" Bata da lafiya ne?" Dan kar ya yi gagawar yanke hukunci a je ba hakaa bane kuma ya saka ITIBEL a wani tunanin daban ASADEEK ya dan yi gyaran murya yana dan jan hanci, sai kuma ya sake waigawa wajen bayin kasa kasa ya ce"Nima fa da mugun zazabin na kwana, ba ita kadai ce take cikin halin neman taimako ba" "Alhamdulilah, Allahu Akbar, Allah gagara misali, Alhamdulilah" SHEIK ke furtawa idannuwansa na neman fitar da kwallah, jikinsa kuwa na daukan rawa Da kyar ya hanna kansa kukan a sanyaye ya ce" Ta yiwu ba wannan ya kawota rayuwarka ba, ta yiwu kuma wannan ya kawota, abinda na sabi koda aurwn soyaya ne sai an lalabasu a rarashesu an yi masu Bauta, ruwa ake tarawa masu zafi ama ka saka hannunka na hagu ka ji idan ya zauna a ciki, sai ka sakata a ciki koda bata so, bayan wannan in sha Allah yanzu zamu zo da Hajia ta boyayiyar hanya zata zo da kayan aikinta ta dubata fa kyau in sha Allah " Asadeek ya dan lumshe idannuwansa alamun amsawa, domin nauyi ya hanna shi maganar gwa da gwa SHEIK ya ce" Kar kowa ya ji, ciki harda UMMA, da HUZNAH, ASADEEK kar kowa ya ji!" Da dan mamaki ya bude idannuwansa, lokaci daya sai kuma matarsa ta fado masa a ransa Me kennan? A hankali ya ce" Har HUZNAH fa kace SHEIK?, HUZNAH ai ya zama wajibi ta san na samu lafiya, domin babu wanda ya cemcenci sannin lafiyata irinta" "Idanfa, dama abinda ke wanzar da rashin lafiyar a jikinta yake?" SHEIK ya fada a hankali ASADEEK ya mike tsaye yana kallon waje daya, ya kasa yarda da abinda yake ji a kunnensa, hakan ya saka shi bada amsa da Uhum kawai ya katse kiran Bayin ya koma, kai tsaye ya tara ruwan ya yi yadda aka ce, sannan ya dawo ba tare da ya jira amincewarta ba tana ta boye boye ko gajiya bata yi ya cicibeta ya kaita cikin ruwan nan ya danata Tun koke kokenta na jiya dai yanzu ta sake fashewa da wani kukan ta rukunkume shi, a dole dai karshe ya shige shima ya rungumeta a jikinta yana dan bubuga jikinta, duda ruwan ya masa zafi shi sosai, ama ba dukansa ya shige ba Hannunta dake tsakanin kirjinsa da nata yake ta ji, wanda ya tokare shi ya hanna shi rungumeta da kyau, hannun kuwa kamar da gangan ta saka shi a wajen, hakan ya saka shi sake zubawa fuskarta ido, yana so ya yi mata tambaya yana jin wani dari dari haka ƙadan a ransa kamar yana jin tsoron amsar da zai samu ta tambayar A hankali ya sake saka hannunsa zai cire nata, kasa kasa ya furta" BAHIJA" Dif ta dakatar da kokowar da take yi da shi na ya saketa ya daina tabata Zaburarun idannuwanta ta dago ta dora a saman fuskarsa A hankali zuciyarta ta karra karyewa, mikin da take ji ya karra sukanta Ita wace riba ta ci kennan a duniya? Wannan mutumen shine UMUGHLUK ITIBEL, tsayayen namiji, zaburaren namiji, zazafan namiji wanda ko ita fa baya cikin layin rayuwarya ta dan namiji ne cikake harda kari, Aban datawa kennan, mutumen da a da tske ba shekaru kusan sittin da wani abu haka, ko sama , domin a yadda ake fadin halaya irin na datakonsa Mutumen da ta shigi gidansa dan ta ankarar da shi abinda yake faruwa a zagaye da shi ta gama ta yi tafiyarta ta auri masoyinta su yi rayuwar aure tare Mutumen da idan ba dan wannan dalilin ba ko me ta taka bata isa ta hango nadin rawaninsa daga nesa ba Mutumen da ko a jiya ta yi niyar idan ta zo zata zo masa da wani rikici irin na sake dora shi saman hanya, sai kawai ta samu kanta da rashin lafiyar da bata taba tunanin tanada ita ba, watau ta hauka, har ta bude masa rigarta tana tunanin Innarta ce? Shine yau ta wayi gari, ita NADIRAH ta rasa budurcinta ma wannan bawan fa bai san wacece ita ba, itama bata san wanene shi ba a banza? To a banza mana bayan aurenta da shi na yan dakiku ne? Shikenan ta fadi a banza? Idan abin nan ya tonu ya gane da baiwa ya raba gado a yadda mahukuntan nan suka dauki bayi ko dabobinsu da suka tsana basu kaisu daraja ba me zai ce da ita? Ita din kankin kanta rayuwar da take yi a tsaye a ra'ayin kanta shi din ba cikin tsarin rayuwarta yake ba, darajarta kwalin kwal da ba'a yiwa mace biyu itace ta rasa? Itafa ba ta balakin da take ji a kasan kasanta ya fi yi mata kunna ba, zata iya rantsewa da wanda ranta ke hannunsa firgicin tunanin nan ya fi komai rikitata Me zata cewa Innarta? Me zata cewa Innar Birni? Da wani ido zata kalli Aban Birni? Idannuwansa ya cire a cikin nata, zuciyarsa na bada wani irin gigitacen sauti mai saka bawa gumi A hankali ya bude ruwan ya ringa tsiyayewa, fatar jikinta ta karra yin jajari ya karra tara wani ruwan yana ji kamar ya rufe idannuwanta dake binsa da kallo A hankali ruwan ya sake hawa jikinsa har ya kai infa yake so sannan ya sake mayar da dubansa tarr cikin idannuwanta A tarihin rayuwarsa zai iya irga sau nawa yake ido cikin ido da mutun haka Ya ambaci sunnan da ba nata bane dan ya ga ko zata amsashi? Ko zata ce wani abu? Ama sai ya ga bata ce komai ba, hasalima kallon da ta bishi fa shi kallo ne mai dauke da kalaman da zuciya ta kasa amayarwa Lebensa ya dan lashe ladan fan ya ji kamar ya mugun bushe masa, Idannuwanta ya ga ta dora saman leben nasa, a hankali ya lumshe idannuwansa yana sake danne kansa, domin ya jima da sake daukan harami, kawai fada dai yake yiwa kansa da fadin ya dace a san kunya da kawar da kai Mikewa ya yi da ita, ya ga yanzu kamar da dan sauki ta dan mike har tana son jan Tawul dake nesa da su kadan A hankali ya ce" Wai da, wankan tsarki zan maki, saboda sallah?" Da sauri ta kalleshi, sai kuma ta cire kanta, kasa kasa sosai ta ce" Sallarma yi mini mana" ta karashe tana gyatsina dan bakinta wanda tsaf ya ji, harda gyatsinen Samun kansa ya yi da sakin dan murmushi a hankali ya cika ruwa a buta ta karfe mai tsafta ya rike yana cewa" Duka na maki tsarkin" A zabure ta kalle shi, sai kuma ta budi baki ta ce" Me kake yi haka? Ka bani ka tafi dan Allah, baka jin kunyata ne? Dubi fa jikinka, ni kuma banida komai haba kaima" Jikin nasa ya bi da kallo, sai kuma ya zuba mata ido Da sauri ta juya tana jin kamar ta nutse dan haushi walahi Sai dai bata san abinda ke yin sababar sababar din na baya shima abin kallon bane domin kallonsa ya saka shi jan numfashi ya ajiye a hankali sannan ya juya yana nufar waje a ransa yana ayyana ' ta yiwu itace ajalina ni kuma, ta yiwu ira zata kasheni, yanzu idan maganar Sheikh gaskiya ne cewa a kanta nake da lafiya a kan HUZNAH bani da lafiya ai na shiga uku, itama kuma ta shiga uku, dan walahi zan ringa ziyartar gonata a kai a kai sai inda karfi ya gaza' Yana fita ta samu ta daura alwallar tana jin du idan ta motsa azaba take ji a jikinta Tana fitowa ta shiga tambayar suturarta Jalabiyar da ya miko mata atafau ta ce ba zata saka ba gaskiya, kayanta take si, bangarenta zata je Du yadda ya so ya dan rarasheta da iya kalmomin da yake da su a bakinsa ta ki yarda, ta kasa aminta, ta ki ta saurara, karshe dole ya koma falo wajen SHEIK da matarsa dake kasa zaune kanta a kasa ya dan kwatantawa Sheikh cewa yarinyar fa ba dai taurin kai ba, wai bangarenta zata je, shi kuma gaskiya ba zai barta ta tafi ba SHEIK ya dube shi ya ce" Kamar yaya ba zaka barta ta tafi ba?" Shima Duban Sheikh ya yi da kula ya ce" Ta yaya zan iya barinta tafia? Idanfa in ta tafi ta gudu kuma yaya zan yi kennan?" Aya, abu biyu ne ya kama Sheikh a irin wannan lokaci, tarin tausayinsa da kuma dariyar lamarinsa Da kula ya ce" Idanfa, a bangaren nata, akoy wanni abin da zai iya kwontar mata da hankali fiye da nan?" Tap, sai ya ga sam Sheik baya fahimta, to mema zai kwontar mata da hankali fiye da shi fisabililahi? Ai baya tunanin akoy abin nan gaskiya, to yanzu shi ta yayama zai yarda wannan mai rawar kan ta fita daga ɓangaren nan? Aa fa, baya son garaje, shekara goma ya yi yana cin wuya, ya dace a gane abinda yake ciki Dubansa ya kai kan Matar Sheikh dake nesa da su sosai, sai kuma ya maido kan SHEIK da sigar bada umarni ya ce" Ka ce mata ta je ta dubata ta sauko ku tafi, ba inda yarinyar cen zata je yau sai ta fada min wacece ita!" SHEIK ya tabe baki ya gyara zamansa, ya kula kam ASADEEK ya yi sake har an ga inda yake da mugun rauni Hankali kwonce ya ce" Ka je ka fada mata mana kai da kanka, kar ta je ta korota ai ka ga kasa take da ita dole ta bi umarninta, ita Matar taka umarninka kadai zata ji a masarautar nan baki daya ko?" Tsuru ya yiwa SHEIK, sai yake gannin kamar SHEIK na son ya nuna yana jin tsoron wancen yar tatsitsiyar? Kai ina shi UMUGHLUK ITIBEL? Shi ASADEEK? shi ANNEMOKAL ITIFAL? 😁😁😁😁😁😁😁😁😁 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 3️⃣9️⃣ Asalamu alaikum, oh 😁, ku yi hakuri kun ji? Kira ne message ne😁, ku yi hakuri, ina cikin uzuri mai girman gaske ne, bana din yanke maku ko yi maku shirme, in sha Allah zaku jini a kai a kai da zarar hankalina ya kwonta, ga daya ba yawa😂 Lebensa ya dantse yana mikewa ya ce" Ham bara ka gani!" Da murmushi Sheikh ya raka shi da kallo har ya bacewa ganninsa, sai kuma.ya maido dubansa kan matarsa da kanta ke kasa baiwar Allah Murmushi ya yi ya ce" Madam ya tafi fa dago kan mana?" Kai ta girgiza kasa kasa ta ce" SHEIK bashida rawani fa, ba zan dago ba ka rufa min asiri" Yar dariya ya yi yana kada kai bai sakata dagowar dole ba, domun ya san yadda mutan garinsa ke girmama shi, kuma dai buzu da nadi aka sanshi gaskiya Da isa ya bude ya shige dakin, sai kuma ya tsaya yana kallonta, jalabiyar da ta ce ba zata saka bace ta saka, ruwan milk Jalabiyar ta amshi kalar fatar jikinta, gashinta dake jike kuwa ya yi wani lufluf a gaban fuskarta Dan cire idannuwansa ya yi yana kallon bed din, yanna nan yadda yake, ya sake kallonta a hankali ya ce" Bafa inda zaki je!" A da ta ki kallonsa ne, a yanzu sak ta dago tana kallonsa, ido cikin ido Kai ta gyada ta taka a hankali ta bude wajen kayansa ta dauko jan hirami dake cikin ledarsa ta bude ledar ta yafa a saman kanta tana gunguni kasa kasa ta ce" Sai ka hannani tafiya!" Kai tsaye ta tunkaro shi, ko nace ta tunkaro hanyar fita, idannuwanta tar cikin nasa, duda tafiyarta dake murgudewa , da azabar da take ji bai hannata dantse lebenta tana masa hararar da ita kadai ta san me take rayawa a ranta, abubuwan kuwa sunna da karfin da a gaskiya ba zata ji tsoronsa ba, jama'a Aminu fa ya sa ta ci amana, Aminunta me zata cewa duniya? Me zata cewa Aminu? Innalilahi wa inna ilaihi rajune Sai da ta zo daf da shi, face da shi, tsayuwar da ta zamto tamkar zata shige jikinsa, ta dago kanta ta sake zuba masa ido kamar yadda yake kallonta da mamakinta, walahi yana matukar mamakin halayanta, ya rasa a wani bigiri zai ajiye yarinyar nan, tunda Allah ya haliceshi bai taba dora magana aka ce da shi aa ba, yana iya cewa wani abin SHEIK kan dawowa ya zauna ya yi ta rarashinsa sannan ya ce da shi idan da hali da kaza ya dace a yi maimakun kaza, to fa ta haka yake samunsa, bayanshi ko Sheikh da yake amini na kud da kud da mahaifinsa baya yi masa haye, ama wannan yar itace ta masa tsaye kikam Shi UMUGHLUK ITIBEL kan sai ta yi abinda ya ce ba za'a yi ba? Idannuwansa ya lumsje, a lokacin da ya ji kamar gumi ke tarin masa a kofofofin hanci da habarsa A hankali ya dan goge saman karan hancinsa sannan ya kauce kadan ya jingina da garun yana kallon ikon Allah Ai kuwa kai ta saka tana dan dafewa a hankali sannan tana rike rigar, domin rigar ta yi mata bululum kamar ta zurma buhu, fadin da tsayin duka ta mata yawa, hiramin kuwa iya saman gashinta kawai ya rufe bai rufe sauran gashin ba Kai jama'a, yau yake koyan darasi, yau gashi ga fitsara gannin idannuwanshi, yace ba inda zata je ta je din, la ha ila ha ilalahu muhamadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallam Kai ya gyada yana daga kafarsa a hankali yana biye da ita, dududu da hannayensa fa sai ya dunkuleta walahi, a kasa take sosai tsayinma da takeda bata kawo ko saman kirjinsa ba, ama take masa kallon cikin ido A wajen saukar na karshe ta yi tsaye tana kallon wajen, domin wajen da dan tsayi gadkiya, idan ta sauko a haka sosai zata fi da jin azaba, kai in bandama kokari irin nata walahi kai sake ba zata iya wannan aiki ba, ama da yake tana da kokari gata ta sauko Daga tsayen da yake a daf da ita ya rage muryarsa sosai ya ce" Ama ai kin san bin miji aka ce a adinance ko ba wai na ringa binki ba ko?" Baki ta tabe tana karra dantse bakinta, mutumen nan ya ki ya gane, ya ki gane idan ta bude bakinta komai na iya fitowa, ya ki ya gane tana rufe bakin ne dan kar dan mutuncin da take tunanin tana da shi a idannuwansa su zube Gannin tana ta son ta duka irin zata zauna din nan sai ta sauka ya saka shi sake gyada kansa yana kifta ido ya zagaya ya mika mata hannunsa mai girma da fadin nan irin na maza da idannuwansa ya mata alamar ta zo Kadadarta ta noke tana hanna kanta fashewa da kuka Ido ya sake zuba mata, a sanyaye ya furta" BAHIJAHHH" "NI BA BA.................." Sai kuma ta yi dif da maganar , irin bara ta mantar da shi din nan sai ta yarda ta miko masa hannun A hankali ya janyoto jikinsa ya cicibota ya daukota gaba daya ya karaso falon da ita Kasa kasa ya ce" A bangarenta za'a dubata" SHEIK da kansa ke kasa shima ya saki murmushi yana sake sada kansa Kara cijewa ya yi yana dan sake tarota, hannunta na wuyansa kanta na kife a kirjinsa, jikinta kuwa zafi ne da shi sosai har huci yake bayarwa, A hankali ya nufi hanyar dake iya sadashi da bangaren nata yana tafe a nutse har ya kawo daf da kofarta Hannunsa ya saka zai bude hanyar ta shiga ta nan din ya ji dumi a gefen kuncinsa a hankaki tana fadin" Ka rufa min asiri ka ajiyeni a nan, kar innata tace na zama yar a zuba ido duniya ta bi da tofi" Dakatawa ya yi, Innarta? Mahaifiyarta? Ko me? Ya Allah, bai taba jin son sannin abu a rayuwarsa irin a kan yarinyar nan ba, yana ji kamar ya bude din ya shige din A hankali ya sauketa a kan kofar da ya san tata ce, domin kofofin hudu ne reras da ake dauka a karasa nasa falon Yana tsaye ta bude ta shiga ta rufo , a hankali ya karra kunnensa ko zai ji wani abu? Ama shiru bai ji komai ba dan haka ya juya jiki ba karfi ya koma falo NADIRAH na shigowa sai da ta cuje dan kwallin ta yar a nan sannan ta gyara tsayuwarta da kyar ta takarkare da karfin da ya rage mata ta fasa ihun da ya saka innarta dake zaune da redio a kafe a kunne tana jin labarin hantsi leka gidan kowa tana dariya da gyada kai ta kafa dauri da sabuwar atampa, domin tunda garin Allah ya waye ta tsinci sarki bai samu sallar asubahi ba ta kada kai ta karra zuba ido yar bata dawo ba ta haye ta tsala wanka ta rangada sabuwar atampa ta kafa dauri, ta tabata alkhairi zata ji da yardar ubangiji! Redion ta wancakalar gefe da sauri ta sauke daurin ta mike tana nufar hanyar da ta ji kukan yar tana salalami da fadin" Wayo ni ta Habu yar nan ina kika kwana?" NADIRAH dake kuka bilhaki a zaune dandabar hannaye kawai take watsawa tana cije lebe da furta" Hummmm, Humm" ta bi innarta da ido muryarta a kurya ta ce" Innata wanka kika yi?" Da sauri Hindu ta girgiza kai ta ce" Wane mutun, ina ni ina wanka, rasa yaya zan na saka atampar nan yanzu nake cewa na je wajen Wancen matar na nemi alfarmar ta rakani wajen Aban bayin Allah na fadi cewa kin bata, innaliwa shigana bayi ya fi a irga yar nsn, tashi mana" ta karashe tana lelen kafafuwan Indi NADIRAH ta sake barkewa da kuka tana kawar da kai ta ce" Ki daina ce masa Aba, walahi bai haifeki ba, ba aban innar birni bane, ba kuma na Aban birni bane?" Wayo dadi, wayo duniya da abin dadi take, da kyar innar Indi ta iya juyar da kanta gefe ta ringa sakin murmushi, yo jama'a in dai Indi ta ga fuskar UMUGHLUK ITIBEL ta yiwu komai ya faru, yanzu baban burinta ta mike tsaye ta dan taka, ta tabata komai kankantar halitar namiji idan ya ziyarci budurwa sai ya nuna, ah to, dan haka burinta ta ga aiki a bayane Da harare ta ce" Ke ba zaki daina yiwa Aban marayu rashin kunya ba ko?, Taso min mana wai daga zaunen nan, yaya aka yi kika biyoma ta nan, ko wancen matar ta rako ki? Kukan me kike yi? Wai wannan rigar ta waye, kuma yaya aka yi ta zo jikinki?" Kukan da take yi ne dif ya dauke, ta zubawa Innarta ido Yanzu Fisabililahi ina ruwan innarta da son sannin yadda aka yi rigar nan ta zo jikinta? Gaba daya sai take gannin kamar Innarta na yi mata wani kallo daban, irin na ta lalace din nan? Kai innalilahi wa inna ilaihi rajune _________________________________ Matarsa ya raka har kofar da ASADEEK ya kwatanta masa sannan ya dawo ya zauna yana ta murmushin da ya gaza barin lebensa Asadeek dake zaune yana dan shan tea din da aka kawo cikin breakfast ya dube shi ya ce" Sai watsa hakora kake yi SHEIK" SHEIK ya yi yar dariya yana gyara zamansa ya ce" Kai kuma dariyar tawa ce take damunka?" Dan shiru ya yi, sai kuma ya yi murmushi shima yana girgiza kai kasa kasa yace" Ban taba haduwa da tsageran da nake jin zan yiwa biyaya ba sai a kan yarinyar cen, cewa fa na yi ba inda zaki, ko irin tace min in barta dan Allah ta tafin nan, kai tsaye ta tunkaro hanyata idona cikin nata, gaba daya bata da kunya SHEIK" Dariya kam yanzu Sheikh ke yi tsakaninsa da Allah, shi dai a haife ya haifi ASADEEK, girma ne ya dame shi kai tsaye bawan Allah, hakan ya saka shi aron halaya irin na manya gaba da baya, ga halin datako kamar wani mai manyan shekaru, bawan Allah bai taba ganninsa da yannayi irin na fara'a haka ba, tunda yake, Haba ya dan dafe ya ce" Kuma kana ji?, Yawanci fitsararun nan sun fi tsaye mana tak a rai, ka duba ka ga maman Safwan, ranar nace kar a min wake a gida bana so, ta yi ta kwaliye shi na rangada, sai da na gama take ce min shine, kuma idona idonta kurrrr sai ni na kawar da kai, kuma har ga Allah na fi jinta a raina" ASADEEK ya yi dan tsam, sai kuma ya yi murmushi ya girgiza kai ya ce" Aa, ni dai ba zata kamo min mar'atusaliha ba, haba dai ai mai jin magana da marar ji ba daya bane, SHEIK yaya maganar nan take ne?, Cewar kar kowa ya sani" SHEIK ya ce" Ka yi hakuri, ka karra bani lokaci, kar wanda ya sani, ciki harda Ummanka na roke ka" Bakinsa ya dan tabe ya ci gaba da shan lipton din nan yana jin yana sake sakar masa jijiyoyin jikinsa ................................................................................................ A hankali ta bude ta shiga tana salama Turus ta yi sakamakon abinda idannuwanta ke ganni HINDU tsaye tana salalami tana bin NADIRAH da kallo wace ke Kwonce tana birgima bihaki tana ihun a kan me innarta zata ce sai ta fada mata rigar nan ta waye Hindu ta bi matar da kallo, mace mai cike da kamala, yannayinta akoy kamala, sai dai duda haka ba zata yi gaggawar sakin jiki ko fuska ba, dan haka ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣0️⃣ Fuskarta ba yabo ba falasa ta ce" Bakuwa muka yi?, Sannu dai....." Sai kuma ta kalli Indi a kausashe da yaren buzanci ta ce" Dan ubanki zaki daina burgimar da iface ifacen nan ko sai na tatakaki ne a gaban wannan, wacece ita ne na ga ta biyo ta nan itama ko hanya ce da kowama zai iya bi?" Murmushi matar ta yi tana dan sake dubansu, zuciyarta ta cika da matsanancin mamaki mai masifar girman gaske, haka kuma Hindu ta bata daria, ko dan ta ga fatarta baka tana tunanin bata jin yaren? Abinda dai ya fi dan cika mata zuciya da tunani shine, Sarauniyar garin Tanut ce akace, kuma uwa ga yayan Agadaz ke burgimar nan ko yaya? Gannin ta ki bada amsa ama kuma ta dakatar da burgimar ya saka Matar SHEIK yin murmushi ta ce" Ki yi hakuri Hajia, dama ni din Matar SHEIK ce, kuma likita ce, na zo dan na duba Uwar Agadasawa ne" Dan shiru HINDU ta yi, matar Sheikh? Wannan kamilalen mutumen da akace sunnansa SHEIK, na gefen UMUGHLUK ITIBEL? Lah ha ila ha ilalahu muhamadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallam, yau gata ga matarsa Murmushi ta saki tana kikifta ido, sai kuma ta kalli NADIRAH dake kallonsu fuskarta na nuna dukkan wani tashin hankali da Rigima a tare da ita yake Yawu ta hadiye, kwarai kuwa abinda take tunanin ya faru fa da gaske ya faru Wayo Allah ga abin rangada buda da dimar rawa ama ba hali Nadirah ta mata tsuru da ido Da sauri ta karasa inda take ta duka ta kamata tana fadin" Tashi mana, mu je ciki, baiwar Allah Bismillah shigo shigo, dan rikici ke damunta, zo mu je dakinta ai in dai dubawar da nake tunani ce sai a daka ko?" Ita dai Matar SHEIK biye take da su, baiwar Allah NADIRAH da kyar take takawa, wajen ne ya karra yin tsami, ga rikicin dake damun kanta mai yawan gaske Bakun makeken gadonta mai kalar gidan sarauta ta zauna tana sada kanta, Inna ta yi murmushi kasa kasa ta ce da Matar SHEIK " baea na barku, zan zaga bayi cikina ya fara murdawa" Da ido ta rakata sannan ta maido dubanta Kan NADIRAH Dan murmushi ta saki ta cire hijabinta da nikaf dinta hakan ya bayanar da nutsatsiyar kamilaliyar fuskarta Jakar ta bude ta dauko safar hannu ta likitoci tana kallonta ta ce" Bismillah Allah ya karra maki lafia" NADIRAH ta dago tana kallonta, Bismillah me? Matar SHEIK ta karasa tana fadin" Baya zaku kwonta sai ki cire wandon ki janye rigar baya na duba da kyau kin ji?" Ido ta zarro da matsanancin faduwar gaba da tsoro Bakinta har yana rawa ta ce" Na cire wandona kuma? A kan me za'a wani dubani? Babu abinda ya sameni fa ni" Ido ta zuba mata itams, karara ta fahimci ko me yake damun Yarinyar A hankali ta zauna cikin yaren French ta ce" Excusez moi, je ne me suis pas présenté, je suis LUBNA MUHAMMAD, je suis la 4eme femme du Cheikh, et je suis médecin gynécologue je suis enchanté de vous connaître et je serais honoré d'être votre médecin " (Ki yi hakuri, ban gabatar da kaina ba, sunna na LUBNA MUHAMMAD, nice matar SHEIK ta hudu sannan ni docter ce a fannin mata, ina farin cikin sanninki, sannan zan kasance cikin farin cikin zamtowa likitarki) 'kan ubancen kayasa' shine abinda zuciyar NADIRAH ke ayannawa a lokacin da ta kure bakin wannan yar gayun dake yi mata yaren aljannu tana makokwaltu da baki tana hirar da sam bata san me take nufi ba har ta dire maganarta tana sake kallonta Wannan lamari ya saka LUBNA dan sake karantar Nadirah Magana ake a kan matar da aka ce ya ce a wajen sarkin Tanut, ba zata taba kawo cewar bata ji yaren da ta yi mata ba, sai dai ko kawai bata yi mata bane Sake sasauta muryarta ta yi a sanyaye wannan karron da hausa ta ce" Allah ya huci zuciyarki, idan har na bata maki ki yi hakuri dan Allah, idan kuwa wani likitan kike so a kirawo bara na koma na sanar sai a kirawo ko wani likita kike so in sha Allah" Kasa kasa NADIRAH na rage girman idannuwanta da sansanyar muryarta ta ce" Likita kuma? Ya min me?" Matar SHEIK ta fuskanceta da duba irin na tsanaki, a hankali ta dan kara matsawa kusa da ita kadan ta ce" ki yi hakuri Hajia, kin san wajen nan waje ne mai matukar hatsari, waje ne da ba'a so a yi wasa da shi, bale ke da iliminki da hankalinki, idan har ya zamto an yi wasa da wajen nan kuma ya raunata akoy katsala, kin ga a wannan fannin ba maganar ka ji kunya, domin ciwo ne, idan ya giga kaine ka shiga uku, idan ya zama gagarare kaine a babar matsala, zai iya gagaraka shiga mutanema bale har ka anfana da shi, yana iya hannaka zaman aure gaba daya, shi yasa nake so ki bada hadin kai a duba ki, a duba wajen dan kowace mace da kika gani ta haka ta girma, wata bata samun matsala kwata kwata, wata kuwa tana samun matsala kadan ne da ruwan zafi kadai ya isa ya warkar da wajen, watan kuwa har tsagewa take yi watau ta damu karuwar da sai an yi mata dinki kin fahimta?" A tsorace ainun, a matukar tsorace NADIRAH ta sake rage amon muryarta tana sada kai irin bata son hada ido da Lubnar nan ta ce" Hala kin san abinda ya faru da ni?" Itama LUBNA sai ta samu kanta da kafeta da ido, a zuciyarta kuwa tana ayana wai me yake faruwa ne?, Turewa ta yi ta fito mata a mutun ta ce" Ba shine sanadiyar kirana ba? Ko ba kin kawo budurcinki bane?" "Innalilahi wa inna ilaihi rajune, wayo na shiga uku kin ga, ki yiwa huwa rahamanu kar ki sanarwa Innata maganar nan, wayo Allahna bayan cin amanar kuma yamadidi ASADEEK zai yi da ni a duniya? Oh ni jikar mutun hudu na ga rana" NADIRAH ta karashe tana riko hannun LUBNA wace ta kusan zurmawa da gudu da ta ji sunnan da ta kama da kukan da take yi NADIRAH ta dora da fadin" Amanatul amana maganar nan, kuma abinda kika fada da yaren ko shima dai maganar wannan din dai ne?" A hankali LUBNA ta shiga tuna kiran da ya samu SHEIK a lokacin da suke zaune shekaran jiya da dare , kasancewar wayarsa ba wani rikaken sirri ne da ita ba, domun sun sha fada masa idan zai yi maganar sirri a cikin mutane ya ringa fita, wayarsa tanada amsa amo mai dan karfin da mutun mai kaifin ji zai iya jiyo hirarsa, Maganar da ta san ta ji daya ce kafin da hannu SHEIK ya mata alamun ta bashi waje, watau *WACECE SUKA AURA MIN?* Sake zubawa NADIRAH ido ta yi, a hankali ta koma ta zauna tana tunani da kuma ba kanta amsa A nutse ta sauke ajiyar zuciya tana sake duban NADIRAH Bata jin French, bata son a san baban abinda kowace mace zata iya yin tinkaho ace itace ta wayi gari a haka, kuma ta kama sunnan UMUGHLUK ITIBEL Ajiyar zuciya ta sake saukewa, a nutse ta yakice tunanin nan, tana karra tanatarwa kanta cewa babu ruwanta a wannan lamari, dan haka sai shiga assuring din NADIRAH, cewa babu wanda zai sani, ai sirrin likita da marar lafiya tsakanin patient da docter ne, sannan ta sake bata hankalinta gaba daya tana sake kwatanta mata girma da darajar abinda ta kawo da kuma maganar dubata, a kalla sun dauki awa ana abu guda, daga karshe ta yarda ama sallar da bata yi ba sai da ta yita kusan sha biyun rana tana ayana ba laifinta bane na maci amana ne, sannan ta zauna gaba daya hankalinta ba wani a jikinta ba, jikinta du ba a sake ba da kyar da walahauli ta iya bude jikinta LUBNA ta dubata Da tausayawa take yi mata bayani kamar Haka" Alhamdulilah baki yi kariwar da sai an maki dinki ba, sai dai kin yi mugun jin jiki ta yadda sai kina shafa maganin da za'a kawo maki sannan kina hadiye na hadiyar, domin wajen daga ciki ya kumburo hakama daga fatar gefe da gefe sannan kin dan karru kadan ba sai an dinke wajen ba, ki samu isashen hutu sannan ku ringa anfani da ruwan dumi kina zama a ciki kin fahimta?" NADIRAH taa gyada kanta kasa kasa ta ce" Ama dan Allah idan an kawo maganin a yi dabara kar innata ta gane" Murmushi kawai LUBNA ta yi , sai kuma ta dauki hijabinta da nikaf dinta ta mayar tana gyara kayanta ta ce" Barana na koma da kaina na amso na kawo maki" Itama ta ji dadin haka , dan haka ta kilacewa LUBNA kayanta a cen cikin adaka ta juyo tana tafiya a hankali sai ga Innarta ta sake faduwa hannunta dauke da kwano yana tururi , watau hanji ne aka rababaka ya samu dahuwa mai daraja yana ta kanshi da tururi Direwa ta yi a gabanta tana fadim" Yi maza rarabakeshi da zafi zafinsa zai fi warware maki yan hanji, yauwana bayin cen akoy irin bahon bayina na wanka ko? Ko sai na dauko katuwar roba?" Naman ta dauka, domin yinwa take ji sosai , saima da ta ganshi ta ji yinwar ta sake sheda kanta ta janyo ta yi bismillah ta fara motsa shi tana kallon miyar da tunanin dama ace ta samu nono ne, da ta morw walahi, ama abin nan idan ka ci ai nauyi zai maka a cikinka sosai Innarta kuwa bata tsaya kulata ba ta shige tana dudubawa Jim kadan ta fito tana kama haba ta ce" Ke bayinki ta fi tawa girma ko me yasa?" Nadirah ta dage kafada tana raunar hanta tana kallon Innarta Wucewa Hindu ta yi ta fice a dakin ya koma kicin dan ruwan zafi ta dora tana gadin ruwan tana dariyar Auntunta, wai daga sanar mata abu sai kawai ta katse kira ta labe🤣🤣🤣, gaba dayama ta ki yarda su yi maganar wai kunya, yo ita yau ai shagali nata walahi, abu ya fara kankama sunna shawara da matar SHEIK? Uhum, Ruwan na fara tafarfasa ta juye a katon bokici ta kinkima ta koma dakin ta wuce ta yi tsaye tana ta tunanin yadda zata tara ruwa a abin nan kamar yadda matar SHEIK tace Kai kawai fitowa ta yi ta koma ta dauko katuwar roba ta kai bayin ta zube ruwan ta sirka shi, ama fa da zafinsa walahi sannan ta fito ta yi tsaye kan yar cewar ta taso maza ta je ta shiga ruwa ta tara mata A wannanma sai da aka yi da gaske, sai da HINDU ta dage sannan Indi ta tafi, haka kuma wajen shiga ruwan da kyar ta iya zama domin ya mata zafi kuma Innarta tace walahi tana sauraronta idan ta karra ruwa zata shigo ta zaunar da ita Ziciyarta na mata suya, tana cike da tsoron shikenan, kennan Innarta ta sani? A haka ta yi ta gama ta fito da jalabiyar tasa tana kallon rigar da Innarta ta ajiye mata ta dha turare Hanci kawai take ja ta saka rigar ta haye saman gadon jikinta da zafi zafi tana sauke ajiyar zuciya Bata jima ba Matar Sheikh ta dawo da maganin innarta kuwa na biye da ita a baya dauke da jarka irin katuwar nan yelow tana murmushi ta ce" Ga nono Indi an turo maki " Ido NADIRAH ta zubawa nonon, innarta ta ajiye ta fita dan dauko abin zubawa A hankali Nadirah ta ce" Waye ya bada wannan nonon?" Lubna dake balo mata maganin ta ce" Daga bangaren UMUGHLUK ITIBEL ne aka kawo" Baki ta tabe bata ce komai ba, ita kuma ta bata na hadiyar ta sha da kyar sannan ta bara mata na shafawar ta tafi ta shafa da kanta tana sake jin kamar duniyar tai mata zafi ita kam, kamar duniyar gaba daya zata kifun mata ne haka take ji Dawowar innarta ya sakata barkewa da kuka , tana jin barci na fuzgarta ama ta riga ta faka garin rigima tana kallon Innarta dake zama tana sallalami da tambayar meye kuma ta ce" Inna, walahu ba zan iya karasa aikin nan ba, ba zan iya ba, gida nake so, innata gida nake s............ *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* '4️⃣1️⃣ Da sauri innarta ta zauna tana ajiye abinda yake hannunta tana furta" Subahanalah subahanalah subahanalah, Indi gida kuma? Mun gama abinda ya kawo mu ne?" NADIRAH ta kwontar da kanta saman cinyar innarta tana wani hakin kukan tana fadin" Ba sai mun gama ba, dan girman Allah ki mayar da ni gida Innata, ba sai mun gama komai ba, kawai Allah zai kare shi, mu bamu isa mu yi masa kariyar komai ba!" Cikin sigar rarashi innarta ta saake tausasa muryarta ta ce" Ama, me ya yi zafi haka da baa wuta ba?, Kyan alkawari fa cikawa, me yasa mun taso mun zo har mun gano wani abu a zamansa da mutanensa zamu zubar mu tafi? Ai hakan ba daidai bane a tunanina, bamu yiwa kanmu adalci ba bale shi mu yi masa, haba kema Indi, me yake damunki ne wani lokacin sai ki rikice kamar ba ke ba?" NADIRAH ta lumshe idannuwanta domun kanta har sara mata yake yi, muryarta a cinkushe, barcin nan na fuzgarta sosai ta ce" Ban zo gidan nan dan wannan ba, Innata ban zo dan na lasance kazar cikin daki ba, kyan alatun dake zagaye da gidan nan baya cikin tsarin abinda ke iya sakani ni NADIRAH na ji zan iya zubar da komai da na gina na farin cikin rayuwata a nan ba!, Innata bana jin zan iya rayuwa a wajen dake zagaye da munafukai mafi soyuwa a zukatan masoyansu ba, hasalima irin haka ya saka nake guduwata wajenku, domin ban.........ban..........innata Aminnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnunnnnnnnnnnnnnnannnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnnn ........" Sadakawar muryarta, daukewar muyarta, da sakuwar jikinta da fitar numfashinta tamkar na dan jariri ya saka innarta lumshe idannuwanta tana sauke ajiyar zuciya da dauke hannunta daga saman kirjinta a hankali tana dan karra kallon Fuskar NADIRAH A hankali ta shafa gefen fuskar nata sannan ta mike kadan ta gyara mata kwonciya ta luluba mata abin rufa ta fice jiki babu karfi ta koma baban falo Tana zuwa falo ta tarar da Umma zaune tana amsa waya kafarta daya kan daya cike da gadarar nan Har ga Allah sai da ta ji gabanta ya yanke ya fadi, jiki babu karfi ta zauna saman kujera ta samu kanta da zubawa Ummar ido tanna kallonta, kallon nan mai kama da kana karantar mutun, kana son gane wanene shi a fasarar badininsa, irin girman waye shi ne a duniyar da ka ajiyeshi Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tana cire dubanta ta dora a kasa Tunda take, bata taba jin tsoro tsoro, firgici firgici, na wannan lamari ba irin na Yau Aminu? A yanzu da wannan gagarumin abu mai daraja ya wanzu, wanda yake abin a wuni yau ana sukuwa da dawakai a cikin fadar nan dan murna da farin ciki, abindaa take cikin tunanin shin yaya wannan bawan Allah yake cikin farin ciki aa yau? Dama tunda ta ji an fadi maganar nan ta cewa Yayarta walahi ita ta tabata lamari ne na sihiri, ita fa ba zata yarda bama ta tura yarinyarta gidaan sarauta babu tsari, mamakin da take yi, mahaifan HUZNAH a labarin da suke tsinta daidaiku ance shi sarki ya auri yar sarakai ne, yaya aka yi suka miko yarinya gidan sarautha baabu tsari? Rayuwar nan da ta zama abinda ta zama yau ko gidan wani dan karamin mai kudi ne ai ks nemi taimako a wajen bayin Allah wa'inda suka riki ayar Allah kan a karra baka daga hasken addu'a tsari dan yaron ya je ya zauna da nutsuwar zuciya, ba wai ta malake miji ko yin yadda aka so da miji ba, aa wannan fa karya ne, ita babu ruwantama da wannan, lamarin karyar?, Shirme ne gaba da baya bata cikin wannan tafiyar gaskiya, ama a yi gyara, a iya girki, a san tsafta, a iya girki, aa iya kisar gyaran aure da iya yiwa namiji hira, uwa uba talabarsa a fagen da daga ke sai shi ki sakashi ihun jariraima watau wannan na kuryar makogwaro mai kama da kukan tinkinyar nan du abu ne da ta rika da karfi take kuma gannin komai hali irin na namiji da ake kadawa ba zata saki wannan ba domin darajarta ce ta ya mace, namiji kuwa ya kada iya shegen mana, ai kowa da irin rawar da Allah ya bashi ikon takawa, in ba dan tsoron kar a mutu walakiri ya mumuke bawa a cikin duhu ba yan rabiya bama ai da ta bi bayan habu, yanna kada gangar tana ana bakace, Firgigit ta dago jin muryar Umma na fadin" Hajia lafia kuwa?" A hankali ta ce " lafiya kalau, na gaa kina waya ne" Umma ta sake zuba mata ido ta ce" Aa gani na yi ina ta magana shiru kamarma baki san ina yi ba?"" Inna ta kade maganar tana yin dan murmushi da daukar kafarta daya ta dora saman daya tana ji a ranta inama idan ta rufe wannan abar da duka za'a gane yarenta? Umma ta sake fadin" Cewa na yi, da nace ba zan ringa yawan shigowa ba, dan na fahimci hakan da nake yi yana hadasa mana rashin jituwa, to ama sai na ga yau gaba daya du irin tsayuwar nan da muka yi a kofar mai baban fada bata leko ba, bayan HUZNAH na tsaye tunda safe sai da wancen munafukin ya sanar mana lafiya kalau muka watse, kin san gidan nan ko me kake yi a ido kake, ana binka ne da kallo ana fahimtar me kake yi, ta haka kake shiga ran bayi idan suka ga mu'amalarka da uban gidanka, ta haka manyan barori ke baka daraja har su ji du duniya kaine uwarsu, mu da muke so mu siye kowa ai ba zamu yi wasa da irin damar nan ba, koda nace zan fita a harkar matse mata waje dan na ga yana neman hadasa mana rashin jituwa, ama dole na ringa lekowa idan ta kama dole, domin na ringa sanar mata manyan sirika irin na sarauta wa'inda bakon gidan nan ba zai taba sani ba" A hankali Inna ta dauke dubanta tana sake tausasa dubanta a kanta ta ce" Hakane, ama sai na ji har kamar hankalina zai tashi da jin wai zaki ja baya dan dan abu ya faru wanda yake abu ne da ko a gida yana yawan faruwa da manyan mutane da ita, jta fa matsalarta kawai kar a shiga gonar iyayenta, idan har ka kiyaye wannan babu mai dadin zama irinta, haba ranki shi dade ina ita ina rasaki a gefe bayan kece uwa kece uba kece makarbiya tata? Kece fa ja gaban tafiyar nan, idan har hakan ya bata maki ki yi hakuri in sha Allah zamu kiyaye, yanzu haka rashin fitarta dan bata sani bane, nan fa muka wuni da ita yanzu barci ya nemi kifata da kas sai ta shige ta kwonta, tana farkawa zan sanar mata fa ga baban sake sai ta je idan lokaci bai kure ba" Umma ta wani saki murmushi, babu abinda ya fi dadada mata sai jadadawar Hindu cewa itace gaba daya tafiyar nan, uhum tana jin dadin ace itace komai fa a waje, tana matukar kishin ace wani ya kamo kafarta ko zai gogi wajen da take sarauniya ce, take mulki a wajen, ba zata taba manta a lokacin da ran mahaifiyar ASADEEK, idan matar na tafe tana take mata baya sai ta ji kamar ta saka hannu ta maidota baya ita ta shige gaban A gadarance ta ce" Na yafe mata, ai ba zan jima ina fushi da ita ba, sai dai a yau kar ta fita, zan san hanyar da zan bi na goge tunanin da bayi ke iya farawa da jama'ar babar masarautar, ai sallar BIYANO ke tunkaromu, zan gani abinda ya dace a yi dan ta karra siyan zuciyyoyin WA'INDA suka isa su fada magana ta yi tsauri" Innarta ta karra gyada kanta ta yi shiru ta koma tunanin abinda zai fisheta har Umma ta gama yatsine yatsinenta ta mike ta tafi A hankali ta koma dakinta ta zauna ta shiga buga wayar Fadime Ta yi bugawa ya kai sau uku da kyar aka daga FADIME na dagawa kasa kasa ta ce" Wai HINDU meye kuma?" Inna ta yi murmushi tana sauke ajiyar zuciya ta ce" Ba maganar abin dadin bane zan maki, maganar da nake son yi maki Aunty a kan Indi ne, kin ga hankalinta a tashe yake, gaba daya rikici take yi wai mu koma gida, ta tsorata da shi ne inaga, kuma bakinta har yanzu yana ambaton sunnan Aminu wai, bana so kai tsaye ta tona mu fa? Kin san Indi kuma idan hankalinta na tashe komai yi take yi" Shiru ne ya wanzu na dan lokaci, a hankali Fadime ta ce" A tsorace take sosai ne?" Hindu ta ce" Gaskiya a tsorace take, domin ban taba gannin cutar da ta kwontar da ita haka ba, kina gani fa ko ciwo take yi tana tsaye a kan kaffafuwanta ne, ama yanzu sai a hankali" "Shi din, ba cewa aka yi bashi da lafiya ba?, Ko ta ji ciwo ne?" FADIME ta fada da kyar kunya na lumlubeta, dan so take yi ta fahimci damuwar yarinyar HINDU ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Kamar baki fahimci abinda na fahimta ba, kamar baki zauna a gidan sarautar ba, ba maganar rashin lafiya, kitumurmura ce ai malan ya fada min!" A hankali Fadime ta sake fadin" HINDU hala banda amsar maganin har wajen boka kika je?" Shiru Hindu ta yi, sai kuma ta ce" Kashhh, a bar maganar kawai ama ba ni na je ba, Habu na aika gaskiya, kuma ban yarda da maganar ba dai, na dai shirya diyata ne shikenan" Ajiyar zuciya ta sauke, a hankali ta ce" Kina ji?, Dole zaki sanar mata cewa ko me yake yawo a cikin kanta ya dace ta daidaita tunaninta ta gyara harshenta ta kiyayi kama sunnan wani da auren wanu a kanta, Dole zata bar maganar nan dan kar ta kona kanta garin shirmenta, Dole zata daina tunda tana jin tsoron Allah taba kuma burin gobe kiyama ta samu sakamako mai kyai, aure ibada ne, ba abin wasa bane, du D'a na halak zai kiyaye yin wasa da igiyar aure, ido zaki murje ki fada mata gadkiya, sannan ki sakata a hanya kawai ki yi kamar baki gane komai ba dangane da yarenta, sannan idan da hali kar zama tare da su ya gagareta, ta koma hanyar da aka dorata sannan ta dora daga inda ta tsaya...." HINDU ta sake sauke ajiyar zuciya, hakan ya saka Fadime a tausashe ta ce" HINDU, na san a gaban matsalar yarki baki da karfi ko dabara, ina so wannan karron ki jajirce kin ji kanwata?" Kai take gyadawa tamkar yayar tata na gabanta, haka kuma ta ji ta samu kwarin gwuiwar tarban yar tata Mikewa ta yi ta koma falon tana ci gaba da tsara yadda ya dace ta biyo da Yar tata dan samun kanta, bama baban rikicin watau komawarta dakin mai babar fada ........................................................... *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣2️⃣ A nutse Sheikh ke yi masa bayani, bayani ne yake yi masa dala dala ta yadda zai fahimta, bayan zamansa a fada da taron da suka gabatar bayan sallar La'asar suka shigo falo, SHEIK ya dube shi yana fadin" Rabonka da zagaye kauyuka irin su Itar, Timiya, titibe ka jima, akoy dukiyarka a cen na kiwo da noma da ake gadi, ka kuwa san garken rakumanka sun zama arba'in da uku a garin Timiya?, Ya dace ka je ka ga yadda arzikin ya yabanya UMUGHLUK ASADEEK ya yi dan murmushi bai ce masa komai ba SHEIK ya sake zuba masa ido a hankali yana kallonsa, a nutse ya ce" Kamae baka jin abinda nake fadi fa?" ASADEEK ya sake dubansa , a hankali ya ce" Allah ya bamu iko" SHEIK ya amsa da amen, sannan ya ce" Maganar da na yi maka dangane da rike maganar nan sirri ina fata kana kai?" Asadeek zai bashi amsa aka sanar da shigowar UMMA Shigowar Umma dauke da wani gora mai dauke da rubutu ya saka SHEIK yin shiru yana kama kansa hadi da maida dubansa wajen TV yana dan kallo duda ba magana dake fita ta tvn sai hotunan larabawa dake karatu kawai Zaunawa ta yi cike da isa ta gaishe da Sheikh bayan ta gaishe da ASADEEK tana cire kanta a barin SHEIK din Kwata kwata a duniyarta ta tsani wannan malamin walahi, mutun ne shi mai shegiyar akida da dan banza iya yi wai shi SHEIK, ta yi kisar, ta bi ta kasan kasar dan ta hadasa masu fitina har ya kore shi ama ya gagara, akoy lokacin da ta so kakaba masa sharin zina karshe ya aure matar ta zama sirri a gareshi, idan ta shigo wajen da yake gaba daya sai ta ji ta tsatsamta da shi, kwata kwata ta tsane shi walahi, wannan fa shine mai yin shahada idan za'a kashe mai aikata laifi irin nata, shine mai jawo masa ayoyi kala kala yana bashi fasara shi kuma yana zartarwa A dan gagauce ta sanar da adadin kudin da take da muradi saboda kicin , domin kiri kiri HUZNAH ta nuna ta amshi kicin din MAI MARTABA, shine ya sanarwa Umma idan tana sha'awar girki bayan na HUZNAr da dayar matar, tana iya fadin dukkan bukatarta a je a siyo ko kuma ta yanke adadin kudin da take da bukata ta bude kicin din bangarenta, dalilin zuwanta kennan har ta biyo masa da rubutun da ta saka ake yi masa na malaka ne wanda cijn ttsafe tsafenta ne dan ta malakeshi tsaf Mikewa ta yi da shek din kudin dake hannunta cike da gadara ana yiwa SHEIK tunkaho ta juya zata tafi, sai kuma ta dawo da kula kula ta ce" Yarona, gaba daya yau sai nake gannin kamar kana cikin farin ciki mai yawa? Ko nice ke tunanin haka?" Murmushi ya yi yana sasauta rawaninsa a hankali ya furta" Alhamdulilah Umma" Sake zuba masa ido ta yi, sai kuma ta ce" Allah ya karra kawo abinda zai kawata fuskarta da murmushi na farin ciki irin wannan" Murmushi SHEIK ya yi bayanane yana gyara zamansa sannan suka amsa su biyun a nutse, Wani kallo boyaye ta sakarwa SHEIK, sai kuma ta fice tana ji kamar ta dawo ta tambaye shi to me ya saka shi farin ciki haka? Sannan ta tambayi Sheik shi kuwa murmushin da ya yi na meye? SHEIK ya ce" Ina fata ka fahimci alkiblata?" Asadeek ya tabe bakinsa yana gyara zamansa a nutse sannan cike da fitar da harufa a tausashe ya ce" Ban san dalilin da ya saka kake karra nanata maganar nan cewa ta zama sirri ba, duda abu ne da ba zan falaso shi doron duniya ba domin sirrina ne, ama kuma abu ne da ya dace ace na wuni ina sukuwa a saman doki a garin nan a wunin yau baki daya dan nuna tsantsar farin ciki da samun yanci, ya dace ace an wuni ana sadaka a bayane ba a boye ba,.....SHEIK ka san na rasa me ya dace ace na kaamanta mata a matsayin karamawa?" SHEIK ya yi yar daria ya ce" Kyauta?" Asadeek ya dan gyada kansa kadan yana cijewa kadan dan yau gaba daya SHEIK bai barshi ya huta ba SHEIK ya ce" To ama, idan aka yi kyauta abin ba zai yadu a fada ba?" ASADEEK ya koma ya jingina, cike da tarin lamari irin na sarautar dake yawo a jinninsa, cike da basarwa tamkar ba zai yi magana ba, ya sake bude bakinsa ya ce " Gaba daya ban ga wanene ya dace mu ji tsoro ko shakun ya ji ba, " Ya dan saurara yana shafa daidai kirjinsa yana jin wani irin yar yar yar a dukkan gabobin jikinsa sakamakon tuno lamarin yarinyar da ya yi, subahanalah wani irun daukaken abu ke ratsa shi ba ji ba gani, a hankali ya sauke ajiyar zuciya ya dora da fadin" Du yadda zaka yi, kana da dama, abu daya ne na sani shine ta cencenci karamawa domin koda kowace mace nada damar yantani ita ta kai ga ci,, Ban sani ba, ita din makashina ce, ko mai tona asirina ce? Koma mecece ita na san tana da baban matsayin da ba kowace ta samu ba, shine zamtowa sirrina, sauran maganar kuma a hannunka ne in sha Allah " yana kaiwa karshe ya mike ya nufi sama dan gaba daya a yanzu sai ya ji yana son tsayuwa a gaban gadon da ya turmusana daren jiya Da kallo SHEIK ya rakashi sannan ya maido dubansa saman cafet yana tunanin me ya dace ya yi, idan ya tuna ba ita bace ainahin Bahija yakan ji tsoro a kasan zuciyarsa, ama yana fadawa Allah ya haska masu lamarin sannan ya kare su da boyayen rikicin dake iya jigata UMUGHLUK ITIBEL Har zai fita ya dawo a hankali ya zubawa gorar nan ido , a nutse ya duka ya dauka ya sake zuba mata ido, sai kawai ya mike ya yi gaba da ita yana dan jujuyata a hannunsa Ficewa ya yi ya nufi gidansa dan Matarsa ta fita, ta je maza maza ta hado abinda ya dace, yana tafe yana ta tsara dukkan abinda ya dace din Daga cen masalaci ya koma ya ja sallar Magariba sannan suka shiga karatu har isha'i ta yi suka gabatar sannan ya koma ya daukota da kansa ya kuma shige falo yana bada umarnin kar wace ta shigo yau UMUGHLUK ITIBEL zai kwonta barci da wuri _________________________________ A falo take a zaune, dadadan turaran wutar da ya gama dakin yana ta fitar da kanshi, gefenta kuwa danyar madarar shanu ce dauke da maganin zahi in ji innarta, ama ta ki sha tana dai kallon TV bakinta a cune tamkar za'a saka masa ribom , ga dukkan alamu a sama take, rigima take ji,jifa jifa kuma sai ta makawa madarar harara ta dauke kai Hindu na murmushi ta karaso hannunta dauke da abin shayi ta ce" Aa, yaya baki sha madarar ba indina?" Madarar ta sake kallo, haka kawai wannan maganin zahi da innarta ke bata ya fara saka mata tunani kala daban a ranta, to wai zahin mema? Kai ina ba zata sha ba, ta yiwu harda gudunmuwarsa wajen neman kasarata da wancen sadaukin ya yi! Shayin ta amsa ta shiga dan kurba bata cewa innarta komai ba, dan gana daya sake nanata hirarsu take yi a cen kasan zuciyarta tana ji anya zata iya kuwa? Baban burinta ta ganta a gefen iyayenta da innarta sunna rayuwarsu a gefe hankali kwonce Innarta kuwa dan murmushi ta yi boyaye tana godiya da Allah da yarta ta sha shayin, uhum NADIRAH kennan a tunaninta a shayin ba komai, bata san shi ya fi daukan abinda zai rikitata ba,da zarar namiji ya tabata kuwa, domin kakarfan maganin tayar da sha'awa ne a cikinsa ama wanda sai an tabata dole sha'awar ko zata tashi, dan kuwa haka kawai ba zai motsata ba Kafarta take dan kadawa tana kallon allon TVn dake karra bata mamaki, TV bango guda jama'a Sukur sukur da kaya alamun ana shigowa ta doguwar biyayiyar hanyar nan ya saka su zubawa hanyar ido su dukansu Bayanuwar matar SHEIK dauke da akwati mai dan girda da kuma karama ya saka Inna mikewa tana yi mata barka da zuwa ta tayata janyo akwatunnan har suka karaso falon suka ajiye sannan matar SHEIK ta duka har kasa cike da girmamawa tana tasbihi ga ubangijin da ya halici wannan halita, watau NADIRAH zaune take da yar riga marar nauyi ta kuma daure gashinta a tsakiyar kanta A tausashe ta furta" Barka da hutawa Gimbiya, Barka da wannan lokaci, Yaya karfin jiki? Ina fata da sauki?" Innarta ta saki murmushi da kafarta ta zunguri NADIRAH dake daf da kafar tata tana fadin" Amsata mana" NADIRAH ta girgiza kanta tana sada kanta kasa dan bata san amsar da zata ba mace mai daraja irin wannan da ta duka tana gaisheta ba Inna ta ce" Tashi mana hajia ki hau sama mana wanna fa kamar ta hadiyi kwado yau, maganar sam bata fitowa daga bakin" Da sauri Matar SHEIK ta girgiza kanta tana fadin" Aa, aa hajia, ba zan iya hawa sama ba, ai idan tana kasa babu wani dake iya hawa sama sai UMUGHLUK ITIBEL " Inna ta dan zarro ido ta ce" To fah Au au au haka abin yake? To bara na diro nima, ke dan kauce kadan na zauna....." Ta sauko din tana dungure kafadar NADIRAH dake sake zumburl bakinta a ranta tana ayana yanzu Innata du wajen nan bai isheki zama ba sai a nan Murmushi Matar SHEIK ta yi, gaba daya yannayinsu sai yake birgeta, har jin abin take a cen ranta A nutse ta gabatar masu da sha tara ta arziki, watau galeliyar alkyaba irin ta manyan matan sarakai da suka amshi sunnansu, sai sarkoki uku na zinari manya da awarwaraye, sai takardun tagwayen gida fa kys din motocin dake cikinsu su biyu A nutse ta furta magana kamar haka" Sako ne daga UMUGHLUK ITIBEL, an ce na gano yaya saukin jiki, sannan na sanar idan ba damuwa gimbiya ta je bangarensa Ido NADIRAH ta zarro ta maida dubanta kan innarta wace karara farin cikin kayan nan suka bayana a fuskarta har kamar ta bushe da daria take yi Baki ta turo ta mika hannu ta dauko dan tuntum din kujerun mai kyau ta yar ta kwonta tana juya masu baya ba tare da tace uffan ba a ranta ta sake ayana' Sai ku daukeni ku kaini na gani' Da mamaki su dukansu suke kallonta Innarta ta sauke ajiyar zuciya tana duban Matar SHEIK ta ce " 🧐🧐🧐🧐🧐🧐 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣3️⃣ Tana sakin murmushi ta ce" Ki yi hakuri dan Allah, yarinta ce" Ajiyar zuciya ta sauke tana sake duban NADIRAH Muryarta ce ta nuna alamun abinda take son fadi daga zuciyarta zai fito A sanyaye ta ce" Dan Allah, ki yi hakuri idan har abinda zan fada zai bata maki, sannan ban sani ba ko hakan ba daidai bane?, Abinda na sani shine dubanmu hakan shine a zuciyarmu, kuma a bakinmuma haka ne" Dakatawa ta yi da maganar tana sake dubansu, gannin Inna ta fuskanceta sosai tana kallonta, ita kuwa NADIRAH ta yi dan tsai alamun tana sauraronta ta ce" Shi din uba ne a garemu, ya kasance mai kwana da damuwarmu a zuciyarsa da kuma aikinsa........, Bari ki ji, walahi shi din bango ne, majinginar talakawa ne,, majinginar masu da shi din ne, Abah muke kiransa, yaro da tsoho" A hankali ta fan juyo ta zuba mata ido, Muryarta ciki ciki ta furta" Yaya kuke kiransa Aba bayan bashi da shekaru sosai a kansa?" Matar SHEIK ta yi murmushi ta ce" Idan kika ga an yiwa ja gaban wata tafia sunna ko wani iri ne, ki dauka cencenta ta saka ya samu sunnan, kuma sunna ne da zai iya fitowa daga bakin talakawa, watau ba daga bakin masu yi masa fadanci ba, shekarunsa basu kai wajen da SHEIK zai duka ya kireshi ABAH ba, ama ko kwanan gobe Humaira Auta takan ce da Sheikh tanna so a kawota wajen Aban SHEIK, a tunaninta mahaifi ne a wajensa domin bakinsa kan girmamashi a bayan idannuwansa ta hanyar kiransa ABAN TALAKAWA, " NADIRAH ta tabe bakinta a hankali ta sake juyawa Matar SHEIK bata yi kasa da gwuiwa ba ta dora da fadin" Dalilin da ya sakani dauko maganar nan, dan na roki alfarmaa ne, dan Allah ki kasance cikon farin cikinsa ko yayane, ki yi hakuri idan har na bata maki " Shiru ne ta sake yi masu, hakan ya saka Innarta budar bakinta da ya yi mata nauyi kadan a hankali ta ce" In sha Allah, ita fin zata zamto daya daga cikin abinda zai kwontar masa da hankali, baki bats mats rai ba, asalima na ji dadin hakan, Allah ya biya, shi kuma Allah ya dafa masa" Da amen amen Matar SHEIK ta amsa sannan ta mike dan tafia Har kan kofar Inna ta rakata tans faman godiya Aa hankali tas dawo ta zauna tana duban kayan, gaba daya ta rasa me zata ce, kayan nan ya zamaa wajibi ta fitar da su cikin sirri tun kafin Umma ta san da zamansu bale har taa nemi sannin dalilin da ya sa aka bata su, gefe daya kuma yannayin y'arta na damunta matuka Muryarta a raunane ta ce" Ama, ina cewa dazu muka gama maganar cewaa kin amince, zaki karra yin hakuri kadan har mu gaa karshen abin nan ko?, Ki duba ki ga tarin dukiyar nan, shin bai cencenci ki yi masa godiya da namijin kokarinsa ba?" Muryarta a mugun raunane ta juyo ta ce " Innata, Innata na yarda fa, nace na amince zan ci gaba da kwatanta bin hanyar da zai fahimci abinda ya kawoni fadar nan, na ce na yarda a gobema zan je na yi zaman da suka saba, ama Innata............" A hankali ta lumshe idannuwanta tana nuna kayan muryarta na mugun rawa ta ce" Innata ama bana tare da irin wannan abubuwan, kayan nan bana so, ban zo dan su ba, asalima ya shiga hurumin da ba nashi bane, a kan me zai lalata min tsarin rayuwata???????" "Bakida hurumin da ya fi shi!, NADIRAH bakida tsarin rayuwar da ta fi tasa, " Innarta ta fada tana tsareta da kakausan kallo Numfashi taa fitar mai zafi, sannan ta ciciba a hankali ta mije tsaye tana jin sosai jikin nata da karfi yanzun Muryarta a rine ta ce " yanada masu sonsa, yanada mai matukar kishinsa, ta isheshi rayuwa, su suka saba da rayuwar nan, ni kam ina jina tamkar a kurkuku, wannan daula bana jinta na fi jina a kule a waje guda, ni ba matar gidan sarauta bace, inada nawa zabin nima, idan har na dube shi....dan kun isa da ni ne!" Tana kauwa karshe ta yi gaba ranta na sake yi mata kunna HINDU ta rasa me zata ce, walahi idan akoy abinda ke matukar dagaa mata hankali wannan rikici da take hangowa a tatare da y'arta Kayan nan ta mayar ta shiga shigar da su dakinta tana tura su karkashin gado kafin ta dawo ta kule ko'ina ta koma dakin NADIRAH, ama sai ta tarar ta yi barci, dan haka ta koma nata dakin ta daura alwallah ta haye saman salaya dan kaima mai duka kukanta, ta san karfinta ko dabararta basu isa su bata abinda take so ba, zata karra kaima wanda ya isa ya gyara batatacen al'amari kukanta , shi zai gyara mata cakulalen rikicin nan ___________________________________ *WASHE GARI* Kamar yadda ta saba shigowa a lati, yauma hakan ce, haka kuma tau a jikin nata babu alkyaba kwata kwata, wani lafcecen hijab ne ta saka har kasa mai hannaye ta fitar da hannayenta sannan ta daure abin daurewar a bayan kanta bayan ta saka baban abin daure gashi, kanshi ne dai take bazawa mai yawan gaske , hankali Kwonce ta ratsa tana tabe baki sanadiyar gannun sun zube kasa kowane kanda a sade ta tabata dan bata da alkyaba ne ba zasu iya yin ido hudu da ita ba Maimakun zuwanta a lati ya kasance sabo a wajensu, sai bai kasance din ba, asalima hijab din dake jikinta ya saka matan zuba mata ido cike da mamakinta har ita da kanta HUZNAH ta kasa dauke dubanta a kanta Dan tsai ta yi tana kallon kujerar da HUZNAH ke sama, wace take zama ce kwana biyun nan, wato ta kusa da shi sosai Kanta ta dauke ta karasa ta ja wata kujerar ta zauna tana dan dago idannuwanta daga lumshe su da take yi muryarta cen ciki ta furta" Sannunku da hutawa" Shiru ne ya biyo bayan tambayarta, ta kai dubanta wajen Auta ba alamun damuwa da rashin amsa matan kasa kasa ta yi mata kallon sannu fa, sannan ta maida dubanta wajen Umma da lamarin yarinyar ya fara tsoratar da ita kasa kasa ta dan sakar mata murmushin da yake a saman lebe ne kawai sannan ta kai kan HUZNAH Duban ido cikin ido suka yi tta yatsina fuskarta wanda kiri kiri ana kallo domin a bayane ta yi sai kuma ta sake maidawa kan wankakun farare tas din plate masu wani tsararen launi a ajiye da rantsatsu cokulai biyu a samansu masu ruwan golding an dan nade su da farin tissu abu dai a tsare masha Allah, sam bata yarda ta dubeshi ido cikin idon nan ba tunda ta zo, hasalima gabanta ke yankewa yana faduwa, kuma zaman da matarsa ta yi a kusan shi ya mata daidai domin koda bata yi haka ba itama yau ba zata iya zama a hakan ba Abincin ta zuzuba cike da isa irin tata itama, harda plate din Nadirar sannan ta koma ta zauna ta dauki cokalinta ta fara ci a hankali Idannuwanta ta lumshe sanadiyar goshinta da ya dauki gumi na zufa kamar zafi ke hura dakin bayan sanyin AC ne ke tashi A jikinta take jin kaifagun idannuwa a kanta, a yannayin kallon mutanen da take yi kuwa sai ta ga babu mai kallonta, ta yiwu wanda bata gaisar bane yake kallonta Murza gaban goshin nata ta yi ta dan dago idannuwanta ta sauke a saman hannayensa , a hankali ta murguda bakinta sannan ta gyatsine hancinta ta mayar da dubanta gefen Auta tana kallonta Idannuwansa ya lumshe hadi da yin murmushi boyaye sannan ya sake duban kalar abincin da aka yi yau, sai kuma ya dubi Auta dake ta faman tsakura ta kasa ci A hankali, furucinsa a nutse ya furta " Bakya son abincin ne?" Kasancewar magana ce ya yi bayan ya dauke dubansa a kan Auta ya saka su kallonsa su hudun baki daya sannan ukun suka dawo da dubansu kan bakuwar cikinsu, domin itace wace t zo masu da firgitaten lamari , kowane yana tunanin da ita yake Da mamaki HUZNAH ta sake dubansa gabanta na yankewa ya fadi da dan karfi, shi kuwa sai da ya dan yanka steek din dake gabansa ya saka kadan a bakinsa ya dan tauna ya hadiye sannan ya dago idannuwansa ya zuba dubansa a fuskar HUZNAH da ta tsatsareshi da ido Idannuwansa ya lumshe mata , sannan ya kkai dubansa kan fuskar NADIRAH Ya taki Sa'a itama a lokacin kallonsa take yi, hakan ya sa suka yi ido hudu da junna Faduwar gabanta ya sakata jin wani irin rauni ya taso mata a cen kasan zuciyarta da kuma gangar jikinta, tana kallonsa jiki ba karfi shi kuma ya saka kaifafun dubansa a kanta, idannuwan da a jiya ta ringa kallo a matsayin wani bijimin zaki, lebunnan da suka yi ta damkar kan mamanta da dogon karan hancin da ya yi ta saukar mata da zazafan nishi a wuyanta A hankali ta dauke dubanta tana tare hancinta da ta ji wani lumlumlum da sauri , watau wani dumi na neman biyowa ta hancin nata wanda ta yi tunanin ko tsinkakiyar majinar nan ce? Ta saka hijab dinta da sauri tana jin kanta na sara mata, wannan wani irin kallo ne yake yi mata haka?, Me yasa take ji kamar zata summa dan faduwar gaba? A hankali ya dauke zazafan idannuwansa daga kanta ya maida kan Auta da ta yi sumnar zaune tana kallon ikon Allah, fuskarsa a sake, sannan a birkice ya ce" Bakya son abincin ne?" Wata ajiyar zuciya ce HUZNAH ta saki da ta fahimci ba da BAHIJA yake ba, Ummama ta fauke dubanta ta yi kamar bata ga komai ba tana jinjina karfin halin NADIRAH Auta ta dan kalli madarar dake gabansa, wa'inda yau abu biyu ne a ajiye a shake da madarar sannan ta sada kanta ta kasa cewa komai *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣4️⃣ Ba edditing fa Madarar ya kalla shima, a hankali ya sake fadin" Dama kina son madara ama baki taba nuna min ba?" Umma ta yatsine fuskarta, a duniya idan ka ji yana magana a tausashen nan yana ta magana dama da mutun biyun nan ne, wancen mugun malamin sai wannan mahaukaciyar kanwar tasa Wani murmushi Auta ta saki tana dubansa da kula ta ce" Abahna, ina son madara sosai, la manta da ran marigayiya ana kawo min madara sosai?" Murmushin ya yi mata shima yana sake kallon yadda fuskarta ke kawatuwa da farin ciki, ya dora hannunsa ya tura mata jug din gabanta kasa kasa ya ce" Da ke, da du wani mai shanye min ga naku" Wannan karron daria ta yi harda dora hannunta saman bakinta cike da mamakinsa, gashi ya yi maganar kasa kasa, kuma ya gimtse kamar ba shi ba, dariarta kadai ta saka su zuba mata ido su dukansu ukun, Huznah da mamakin wai Auta ce ke daria?, Umma gananta ya fadi tana sakw duban Auta zuciyarta na shiga a uku da gannin daria ne take yi? Na menene? , NADIRAH kuwa ta zuba mata ido tana kallon dariar tata wace ta sakata jin kamar zata saki murmushi domin kana kallo zaka ga abinda ya sakata dariar mai girma ne a zuciyarta Hannunta ta cire wanda ke tare a gaban hancinta zata duba ta ga ko menene Da sauri ta zarro ido tana mikewa tsaye hakama Auta fa sauri ta furta" Subahanalah aunty Jinni ne?" Ihu NADIRAH ta saka ta tataro hijabin nata gaba daya ta cireshi tana karra saka ihu tana fadin" Na mutu jinni wayo Innata jinni, wayo jinni na mutu daga ina yake fitowa?........." Sumurta kokowa take yi da kanta tana cire hijabin gaba dayansa ta bayana daga ita sai zani daban riga dabsn, rigar mai siririn hannu, zannin kuwa ta masa wani dauri a cen saman gwuiwarta gashin kanta a daure a tsakiya ta ringa kai hannunta tana shafowa ta karra kwala ihu tana fadin" Na shiga uku Habo ne, walahi habo ne nake yi............................" Mutun biyu suka zabura suka nufota watau Auta da Umma, HUZNAH kuwa ta rafka tagumi tana tunanin anya tunda yarinyar nan ta fara cin abinci da su an taba zama aka wanye lafiya?, Shi kuma a hankali ya jingina da jikin royal kujerar ya zuba mata ido yadda take sumurtu tana kwala ihu tana gudu ta ki tsayawa bale su Umman su iya riketa karra fadi Take yi INNATA HABO NAKE YI A zabure ya mike tsaye daga zaunen da ya yi a lokacin da ya ga tsutsar kan nata zata izata waje a haka Taku uku ya yi a hanzarce ya damki hannunta na dama ya janyota gabansa sosai yana son dago fuskarta ama ta ki yarda da hakan sai zunduma ihu take tana a taimaketa habo take yi Umma dake fadin" BAHIJA ki saurara mana, tsaya a duba mana, ki daina dukar da kanki ba zai tsaya ba" ya duba a hankali ya furta" Umma, je ki ci abincin bara na wanke mata" Da mamaki Umman ta dakata da son rikotan tana kallon yadda ya saka hannunsa ya cicibata gaba dayanta ya dora a kafadarsa ya juya ya nufi hanyar sama da ita a lokacin kuwa bakinta fadi yake" Umma amsoni, umma dan Allah amsoni, UMMA kar ya tafi da ni, UMMA ki amsoni" Sunna tsaye kamar a summe su biyun haka matarsa na tsaye a gaban abincin tana hangensu har ya bacewa ganninsu sannan Umma ta juyo tana sake zarro idannuwanta sai idannuwan nata suka sauka a kan HUZNAH da ta yi wani iri kamar zata fashe da kuka tsabar hankalinta a tashe yake Dan murmushi ta samu kanta da saki, tabas idan har ta yi la'akari da maganar da yarinyar ke fada mata cewa ta barta ta yi aikinta yadda ya dace ya dace ta bartan, domin idan har hakan ne tabas yarinyar zata yi gagawar kaisu ga ci a mafarkin su, dan haka bara ta jefi tsuntsu biyu da jifa daya ta hanyar gumawa matarsa ta kasheta da kutu Zama ta yi saman kujera ta sake janyo abincin ta saka cokalinta hankali kwonce ta sake kallon HUZNAH dake kallon hanyar da ya bi da NADIRAH ta yi murmushi ta ce" ki zauna mana Gimbiya?" Gabann HUZNAH sai da ya karra faduwa, a hankali ta juyo tana kallon Umma Gimshewa ta yi tana kokarin boye damuwar dake shinfide a saman fuskarta ta zauna tana kokarin ci gaba da cin abincin Umma ta sake yin murmushi tana hangen Auta ta tafi falo ta zauna a ranta ta yi kwafa, a bayyane kuwa ta ce" Kin san ita fa mace, mai sunna mace bama sai ta zuba leshen daruruwa ta maka hodo a fuska ba ake kallonta, kuma ba zaki taba ganninta tana fadanci dan a dubeta ba, ita fa mace ginaniyar mace tana zamanta a daki za'a zo a roki alfarmarta, a rarasheta, a roketa ta amshi kudade sannan a kireta gimbiya........, Ita mace mai daraja ba ita ke roka ba, kuma walahi namiji ko ya ki ko ya so dole ya bata kudi da katsayi dan cencenta ce abin ai" Sosai maganar ta soki zuciyar HUZNAH, kanta a kasa yake tana ta sake danne zuciyarta dan kar ta yi abinda ba shi ba, ama sai ta ji ta kasa, , ba zaku gane bane, abinda ya shafi mijinta na fin karfinta, du yadda zata yi dan ta kaucewa abin sai ya zo ya zame mata damuwa, domin yana fin karfinta ne sosai, bata san yaya aka yi abin nan yake neman cin mata ba, abinda ta sani shine lalle an soketa a wajen da bata iya hakuri A hankali ta dago tana kallon fuskar Umma, Umma dai fara ce, ama a idannuwanta ganninta take yi tamkar kumurci bakin maciji mai bakin kwali Gana daya matar babu fara'a ko annuri a fuskarta sai tarin bakin fencin dake bayana a koda yaushe a tatare da ita A sanyaye ta ce" Hakane, kowace mace da irin tsarin rayuwarta, matar si dinma ai kala daban daban ce, wata macen wanda zai dubeta da maganar so dinma bata samu , komai matsayin da take gannin ta taka a duniya, komai girmanta da arzikinta sai ki ga ta koma ga ubangijinta a haka..................." Ta ajiye maganar a hankali tana cakular abincin Umma ta kureta da ido cike da mamaki, muryarta na cenzawa ta ce" HUZNAH nice zaki yiwa rashin kunya?, Nice zaki zaga?" HUZNAH ta sake dubanta itama ta ce" Ba maganar zagi, magana ce ta rike mutunci, idan har kin yi komai wulakantani da zaki yi zan jure, in kuwa ba haka ba kina iya gannin ba daidai ba Umma, akoy jifan da idan aka yi min bana iya hakura, shine wanda ya danganci mijina, ina son abina, zan kuma rayu da kayana a kowani hali!" Umma ta tabe baki, sai kuma ta yi murmushi tna yin kwafa ta ce" Hakane kuma, maganarma da kika yi gaskiya kika fada, wata macen kuwa yadda ta zo haka take komawa, ga mijinma a gefenta ama kuma ba wani katabus sai bakin ciki?" Daga haka ta mike tana kallon abuncin a raine ta ce" Kin amshi kicin kuna ta faman hadamu da kayan fulawa, ya dace ki yiwa kanki fada ki kuma ba mai waje wajenta ta huta, koda yake kamaninki kamanin ta kicin ce, Gimbiya kuwa sai kafadar UMUGHLUK ITIBEL!" Tafiyarta ta yi cike da gadara, tana zuwa falo ta tsaya gaban Auta wace ke zaune tsuru tana ta addu'a a ranta Kasa da sama ta kalleta ta watsar ta ja tsaki sannan ta ce" Ki ci gaba da take dokata, ke kin san wacece ni, kin san na yarda da maganar ba zan hada maki sharin kina kwana da mace bane dan kina min biyaya, ki yarda ki take dokata sai na baki magani kin bugu sannan na tura yarinyar da zata yi maki zigidir ta gama abinda take so da ke ta kuma yi kukan kin afka mata, ai jaraba gadon gidanku ne, ko shi yayan naki na san a hannu yake kwana da wutsiya yana ihun a bashi mace ya farwa, sai dai kuwa ya mutu ba shi ba jin dadin mace!" Daga nanma ta fice ta bar Auta jikinta na rawa tana kallon hanyar da ta bi Zaunawa HUZNAH ta yi a gefenta tana kallonta, sai take gannin kamar da hankalinta, A hankali Auta ta dubeta, sai kuma ta janye dubanta tana ta Adu'ar tana jin nutsuwa na ratsata sanadiyar ambaton Allah A hankali HUZNAH ta sake duban hanyar sai kuma ta sauke ajiyar zuciya kasa kasa ta furta" Allah ya yi mana maganinta!" Surmiyowa take son yi ama ko alamu ta kasa har ya karasa bayi ya bude da hannunsa daya ya shiga da ita ya karasa gaban ruwa ya dauko kan pampo mai igiya ya dan danna shi a hankali ya shiga wanke mata bayan ya tareta da kafarsa daya ya hannata zugawa da gudu Fuskar ya wanke sosai sannan ya kamata a nutse ya dan dage kan yana dan sake tareta a jikinsa kasa kasa ya ce" Ke kam ki tsaya mana" NADIRAH ta rintse idannuwanta sakamakon hucin numfashinsa dake sauka a fuskarta Muryarta a raunane ta ce" Ka barni mana kaima menene haka?" Fuskar tata ya zubawa ido yana ta kallonta, a haka din ya ce" Ba zan iya barinki ba" Baki ta turo tana gungunnin da ya sakashi zubawa fuskar ido cike da mamaki yana son dole dole sai ya ji abinda take fada, ama ya kasa ji Wanda ya dan taho ya kanjace ya tare hanyar ya dan goge mata sannan ya dago kan nata Gannin zata dukar da kan ya saka hannunsa ya dago fuskarta yana kallonta ido cikin ido ya ce" Me yasa zaki dukar da kanki bayan na sani kema kuma kin san ba tsorona kike ji ba?" Ido ta warro a saman fuskarsa sai kuma ta sake turo baki ta ce" To ka dan matsa mana ka matsen waje baka gani?" Bakinsa ya dan tabe ya ki katsawar, hasalima rawaninsa ya shiga saukewa hakan ya saka gabanta faduwa tana kallon hanyar fita sannan tana kallonsa a sace tana dan matsa kafarta a dabarance har ya sauke rawanin ya rataya shi jikin abin shanya sannan ya fara yin gaba ya fito a bayin ya tsaya yana kallo ta fito ta nemi zagayeshi sumui sumui zata fice kasa kasa ya ce" Yaya aka yi jiya baki dawo ba?" Turus ta yi tana jin wani haushi haushi na turnuketa Juyowa ta yi a hankali tana dubansa , ta samu kanta da fadin" Me zan yi maka idan na zo ni kuma?" Idannuwansa ya dan buda irin oh really? Din nan, sai kuma ya dubi gaban rigarta da jinnin ya bata sannan ya zubawa gaban rigar ido da kyau yana ji jikinsa na neman birkicewa Da sauri ta juya tana kallon kofa tana auna irin gudun da zata arce da shi dan barin dakin wannan mutumen A zabure ta rintse ido sakamakon jinta a jikinsa ta baya A birkice ta juyo ya kasance ta shige kirjin nasa gaba dayanta sai kuma ta dago ta saka hannayenta dan yin kariya da hannunta da kirjinsa, muryarta a raunane ta ce" Ka bar min irin haka dan ALLAH" "Yaya zaki tambayeni me zaki yi min bayan kina tare da abinda yake nawa? ............." Ya fada a tausashe , sai kuma ya dora hannunsa a hankali ya dan shafa bayanta yana lumshe idannuwansa a hankali ya dake fadim" Wai da so na yi na sake tsoma lipton dina a cikin shayina" Ido ta rintse wata masifafiyar kunya na tasowa tun daga kafafuwanta ta rufe har kanta Hannunsa da ta ji a wajen cinyarta a hankali ya sakata dora kanta saman damtsen hannunsa a hankali ta sauke sansanyar ajiyar zuciya sannan ta dago idannuwanta ta zuba dubanta a saman ni'imataciyar fuskarsa tana kallo Hannunta ta dago a hankali ta dora a gefen fuskarsa mai dauke da ni'imtacen sajen dake kyali na duhu da tsarinsa ta dan shafa tana kallon karan hancinsa har zuwa jajayen lebunansa masu kama da fitsararun lebe Idannuwanta ta lumshe a hankali ta ciro harshenta tana dan lasar lebenta da take ji kamar ya bushe mata kauuuuu dan wata bakuwar jaraba A hankali ta ce " LIPTON din ne naka Aban datawa....................., Aban datawa kai baka san ba'a wawurar nama daga ganninsa ba?" Wata irin ajiyar zuciya yake saukewa, jikinsa na saki gaba daya yana sake dubanta, subahanalah haukatashi aka aikota yi ne? A gaskiya wannan yarinya koda zuwa ta yi dan ta kashe shi ya shirya ya sakankance kawai ta auna masa ko meye ta morw abinta, ai ko a haka ya tafi kam ya ga mata gannin idannuwansa Muryarsa ta riga ta koma cen cikin makoshinsa ya ce" Shi nama, idan naka ne, ai kana da damar ci a duk lokacin da bukatar hakan ta motsa maka ko?" A hankali ta cire dubanta dan haka kawai sai ta ji kan mamanta ya fara yi mata kaikayi, yau ita ke karra gannin sabin salalamen rashin da'a a jikinta A hankali ta dan janye jikinta baya tana jan rigarta ta rufe da kyau ta dan juyar da bakinta gefe ta ce" A daina kwace" Ido ya dan zarro yana tsaye irin tsayuwar nan da ake dan wara kafa, so yake ya tambayeta shin wacece ita? So yake ya san kadan daga cikin lamarinta, ama SHEIK ya wani dakatar da shi A hankali ya ce " Bafa kwace na yi ba, cewa kika yi na kama, da kyar na yarda fa" Ido ta zarro tana shagwabe fuskarta kamar zata fashe da kuka tana kallonsa, hakan ya saka shi sake zuba mata ido, yana girgimama sarautar mai sama, yanzu dai wannan yar dukus din nan ce ta ga manya a yadda ungozoma ta mikowa GIMBIYA , gatanan abinta idonta idonsa, gaskiya mata Allah ya masu baiwa Juyawa ta yi a hankali ta nufi hanyar ficewa hakan ya saka shi dan karkata kansa yana kallonta muryarsa na dan fita ya ce" Ina zaki je kuma?" Dakatawa ta yi , sai kuma ta juyo tana nuna masa kasa kasa ta ce" Ka manta matarka na kasa?," Dan sake zuba mata ido ya yi, abinda ke zuciyarsa nada yawan gaske Juyawa ta yi ta kama abin budewar tana kallin girman abin budewar kasa kasa ta kuma cewa" Bayan wannan, aikin da kake son bani, ba shine aikina ba......... Shi nama ai kanada da yawa, ya dace ka barawa wani nasa!" Rufewar dakin ne kawai ya fargar da shi da tunanin da ya auka na furucinta, Ba wannan aikin ta zi yi ba?, Ya dace ta barawa wani namansa? Me kennan?................ .............. ........ Readers me kennan?☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️ *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣5️⃣ Ku karra hakuri jama'ata 😁 in sha Allah saura kiris na dawo daga hutu A hankali ya karasa bakin bed din ya zauna yana sake kafe waje daya da ido Ba wannan aikin ya kawota ba, shi nama ya dace ya barawa wani nasa?????????? Gefen mataunansa ya dan cije, hakan ya sa kashin gefen fuska dake boye bayana ƙadan ya nuna alamun abinda ke cikin zuciyarsa Ya barawa wani namansa?, Ba wannan bane ya kawota?, Anya zai iya hakura har sai an nuna masa abunda ke wasa da hankalinsa kuwa? A hankali ya sake lumshe idannuwansa, yana ji a cen kasan zuciyarsa anya zai iya ja da wannan rikicin kuwa? Bai san rikici irin na cen cikin zuciya ba, wanda ya sani na fili ne, a bayane, wanda zai ja tunga ya daka da kaffarsa a suma, ba irin wannan ba wanda yake daidai da boyayoyina da makaho Safarsa ya cire ya dora kafafuwansa ya sake harde hannayensa yana jin jikinsa na ta neman rikice masa 'Ama me yasa zata yi min haka?, Na yi mata wani laifi ne? Bata san girman hakina dake kanta bane?, Ko bata gane a kanta na san lamarin bane? Ya dace ta zamto mai tausayi da jin kai a gareni, domin nima ai mutun ne, ko laifi na yi mata ya dace mu zauna mu yi bayani ko?' yake ta ayana a sanyaye cikin zuciyarsa, jikinsa kuwa banda sake rikicewa babu abinda yake yi, a yanzu bai san me zai yi tunani a kai ba, shi dai ba zai ce bai san so ba, domin matarsa uwar gidansa soyaya da yarda ke rike da mu''amalarsu, da babu so da tausayi da jin kai da sun raba hannu a yadda suka kasance mararsa anfani ma junna, haka kuma shi ya san cewa tsakaninsa da wannan yarinyar babu maganar so , yana dai tunanin abinda ya sa yake matukar jin kamar numfashinsa zai tsinke idan yace zai zauna ya zurfafa a tunanin son gane wacece ita?, Me ta zo nema rayuwarsa?, Tana daya daga cikin masu neman gannin bayansa? Idan har haka ne to shi yaya zai yi da rayuwarsa? Zai iya fadin yana ji a zuciyarsa sai dai su kashe junna shi da ita, yana jin a ransa cewa a kanta yana iya tafka aikin da za'a ga rashin wayonsa, gata yarinya karama duda bai san shekarunta ba, gata yannayin wajen da suka fito ba iri daya ba domin a bayane yake ita din ba jinnin sarauta bace, kai lamarinta na hadasa masa ciwon kai mai tsananin gaske............... Da farko a zabure ta fito da gudu gudu ta nufo matatakalar saukowar tana waigen bayanta gabanta na faduwa tana Adu'ar Allah ya shiga tsakanin na gari da mugu, watau ita da wannan bawan Allah Tana hango matarsa zaune da kanwarsa ta ja ta tsaya tana sauke numfashi wani na korar wani tana daidaita kanta da tunanin abinda ya dace ta aikatawa matarsa dan ta karra dorata a kan layin mijinta cikin dabara ba a bayane ba Tafiyarta ta daidaita tana kin kallon jinnin dake gaban rigarta a ranta tana ayyana cewa' In sha Allah, na kusa gamawa, in sha Allah na kusa, ba zan tsaya sai sun banu damar sanar maka wacece ni ba , zan kwatanta maka ta yaren da na fi iyawa, zan kuma ganar da kai a aikace idan ya so sai ka kashemu dan mun shigo maka rayuwa!' "Ana hutawa?" Ta fada a hankali a lokacin da ya rage mata matatakala biyu ta idasa saukowa bayan ta dafe hannunta a jiki ta yi wani iri da fuskarta irin yannayin nan na raini A tare suka zuba mata ido sunna kallonta, irin kallon nan na karewa mutun kallo, bama kamar Bahija da sai da ta ji gabanta ya tsinke ya fadi da karfin balaki ta zubawa NADIRAH ido NADIRAH ta dan tabe baki tana jan hanci ta kalli sama, sannan ta sake kallonsu ta idasa saukowa ta karaso fallon tana kallonsu kasa kasa ta ce" Ama ai dai ba sai an ce maku ku tafi ba ko? Fisabililahi mace da mijinta a ranakun amarci a ringa sakata a gaba ana mata ido ido kamar an kama kwartuwa?, Ni kam wannan lamari nakunyana daure min kaina, ta yaya za'a ce du dare na Allah a ranar da take taku ko ba taku ba sai kun zo kwayakwayanku da kwarkwatarku kun sakan miji a gaba kunna ci yana ci an hanna ni yar soyyayar da abina?, Sam wannan tsari baya birgeni, kuma na dakatar da shi!" Ta idasa tana hade girar sama da ta kasa tana duban HUZNAH da ta wara idannuwanta da suka sha kwali mai kyau tana yiwa bakuwar jarabar da ta risketa fashin baki dan ta gane irin jarabar da zata kasheta ne ko ta jigatatata? Yau ita Huznah wata mace mai daura zani zata koyawa zama da mijinta ko cenza tsarin mijinta? Muryarta a hade ta sake dubanta da kyau, kafin ta mike tsaye tana dubanta ta ce" Ina gannin baki gane abinda kika tarar ba ko? Wama sunnanki? ....." Ta isada tana kallonta da kyau, sai kuma ta tabe bakinta ta ce" Ba wannan ba, sunnankinma ba shine a gabana ba, ina so na fahimtar da ke cewa da kika samu mijina yanada igiyar wata mattar a wuyansa, haka kuma in me kike takama da shi nima ina takama da shi, So ki iya bakinki da take takenki, ki kama kanki ki daina zubarwa mijina mutunci kina abubuwa kamar wata wace bata san NOBLESSE ba!, Kina saka sutura kamar zaki je gada kina fitowa ba alkyaba ba, na kasa fahimta menene a cikin kwakwaluwarki mai zafi dake juyata haka ba, abinda na sani shine babu macen da zata shigo gidana ta lalata min farin cikina da zamna da mijina, babu macen da zata nemi hautsina min lisafina!, Maganar soyaya kuma da kike yi kece bakuwarta, ina tunanin abinda wasu matan suka ci a kan soyaya ke ba zaki taba jurewa ba!, Ban iya fitina ba, ban iya rikici marar anfani ba, kar ki koya min dan Allah domin a kan mijina kadai nake zamtowa wawa har na daga muryata!" Ta karashe ranta na sake amsar gayatar NADIRA, wace ke kallonta hankali kwonce tana dan murmushin nan mai karra tafarfasa zuciya A hankali NADIRAH ta kalli Auta da ta mike fuskarta na nuna hankalinta na neman tashi sanadiyar abinda take ganni wanda ba zata so ace yana faruwa a cikin gidansu ba, bata san dalilin da ya sa take ji a cen kasan zuciyarta bata so haka ta fara faruwa da su sam, ba dan tana shiri da HUZNAH ba, ba kuma dan sun shaku da NADIRAH ba Murmushi ta yi ta dauke dubanta ta maida kan HUZNAH, a hankali ta ce" Kina ji, maganar Alkyab da wani wai shi nozlasssss ko me? Ke ta gano!, Yanzu Kina tunanin dan ina bakuwa a gidan nan na zamto bakuwa a duniyarki da ta mijinki?, Ai mace ko yau ta shigo gidan miji ta tardo mata uku ta zamto ta hudu sunnanta mata a cikin gidan kuma za'a kirayeshi mijinsu ba nata ita kadai ba, ko a rikicin kishinki a kan mijin naki kin manta wannan ne?, Mace kuwa, wace ke gidan mijinta, kina so ki ce min idan zata yi tsari na tsakaninta da mijinta sai ta nemi shawarar uwar gidansa dan tana wa?, Abinda yake farin ciki a wajenki ni shirme nake kallonsa, ko mace maki hauka nake kallonsa! Ki yi hakuri ba zaginki nake yi ba ko raina ki, gaskiyar abinda nake so a kiyaye min na fada da babar murya, daga yau bana so na kuma gannin kafar mace uwa ko kishiya ko kanwa a lokaci irin wannan idan kwanana ne a bangaren mijina!, Sunnan hakan sannin ciwon kai da iya kula da Namiji, kin ga idan kunna zaune na mika kafa na lalubo ta ASADEEK ai an yi abin kunya ko?, Gashi da sauki cafka....ke kin sani!, Bana son yin rashin kunya shi yasa na fi gane na yi bayani a saukake dan ku fahinta, saurana kwana uku mu dawo raba kwanaki, hakan na nufin gobe kina da damar gannin mijinki cikin wuni, da zarar dare ya yi a bar ASADEEK ya dan zaga ko zai iya wartar linzamin doki da karfinsa!" Subahanalah, Hasbunnalahu wani'imal wakil, wannan wani irin tashin hankali ne, jikin HUZNAH har rawa yake yi tana kallon NADIRAH Hannunta ta saka ta ja NADIRAH da karfintta ta mayar da ita gefe sannan ta shiga Haurawa sama har tana hade bibiyu tsabar hankalinta ya tashi, idannuwanta sun rufe, kai ba'a yi ba, ba za'a yi ba yar da zata zo ta wulakantata, zata je ta same shi a yita ta kare, ita ta san waye uban gidanta ba zai taba bari wata halita ta wulakantata ba a doron kasa ba tare da ya kare yancinta ba! Idannuwanta a bude kasa kasa ta ce" Toh fah, bara na gudu wajen Inna kar a ci zalina" Gana juyowa suka yi ido hudu da Auta, wace ke tsaye tana kallon ta, kallo irin na tsoro da mamaki Idannuwa ta fan kifta sannan ta zagaye a hankali ta nemi hanyar tafiyarta tana ta neman hijabinta fa idannuwanta "Auntu BAHIJA" Auta ta fada a sanyaye tana sake dubanta Turus ta yi da son tafiyar, tana ji a ranta wani abu na tabaa zuciyarta sakamakon muryar Auta da ta ji na rawa A hankali ta juyo tana kallonta, Auta kuwa ta sake kura mata idannuwanta da suka cika da kwallah a hankali ta ce" Aunty Bahija, har nima na daina zuwa wajen Abahna?, Aunty idan ban zo ba a cen take bani abincin cike da kayan maye, dan Allah kar ki hannani zuwa wajensa kin ji?" Wani irin duka zuciyarta ta yi, a hankali ta ji zuciyarta ta wani irin mugun karyewa ta shiga bin hawayen dake zuba a saman fuskar Auta da kallo Bata taba jin zuciyarta naa neman sakata a uku ba irin na yau da ta ji kamar zata fashe da kuka sanadiyar damuwar yarinyar dake bakuwa a duniyarta Kanta ta cire, idannuwanta suka sauka a kan hijabinta Da dan sauri ta karasa ta dauka zata saka ta sake kallin jinnin gaban rigarta, hakan ya sa ta zagaya baya wajen kujeru ta raage tsayinta sosai ta cire rigar sannan ta saka hijabinta ta dago a hankali tana satar kallon Auta a ranta tana jin tsoron hada ido da ita dan bata son irin wannan sensation din mai girman gaske a rayuwarta Ido hudu sula kuma yi, Auta na tsayen nan tana kallonta Kai ta sad ta ja numfashi tanaa dantse lebenta, zuciyarta na yi mata rawa kamar zata ballo ta fito Rasa bin yi ya sakata zagayowa jikinta ba karfi ta zauna a saman kujerar tana kallon Auta A hankali Auta ta ringa takowa har inda take zaune ya zo ta zauna daf da ita tana kallonta, ita kuma ta daina kallon nata dan ji take yi har a ranta kamar zata fashe da kuku A hankali Auta ta dora kanta a gefen kaffadar Nadirah, sai kuma shshekar kukanta ya yawaita, muryarta a cakule ta ce" ke fa kika ce min na yi yadda zan ji sanyi? Sai kuma kice kar ki kuma gannin ƙafafuwanmu a gefensa?, Aunty Bahija shine sanyin namu fa, a gefen nasa ne muke da rangwamen tsana da neman halakamu da ake yi, kafin na gane da kayan maye a abincin da take bani na jima Aunty, shi yasa da na gane nake guduwa nan domin na ci a cikin nasa duda na san bai dace ace kowani dare na zauna da matarsa na ci abinci bayan ni din ba wata yarinya karama bace, sai dai tsoron abinda ke wajen hakan ya fi komai yin tasiri a rayuwata aunty Bahija, kin ga itama aunty HUZNAH bata da rigima dan Allah kar ku ringa yin fada, walahi ni ina so ku zauna da Abahna ku dukanku, dan Allah kar ku ringa yin fada" Idannuwanta ta karra lumshewa tana jin yadda zuciyarta ke bugawa a hankali ta kai hannunta gefen fuskar Auta a hankali ta dan shafa gefen fuskar sai kuma ta maido hannunta ta ajiye tana sauke ajiyar zuciya So take yi ta yi mata irin na ranan nan ama gaba daya ta ji bata da karfin hakan, Muryarta a raunane ta ce" Dan Allah, zaki iya sanar min wacece UMMA a rayuwarku?" Dgowa Auta ta yi tana kallonta da dan mamaki a saman fuskarta Muryarta na fitar da amon mamakin ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣6️⃣ Muryarta na fitar da amon mamakin tambayarta ta ce" Aunty? Baki san wacece Umma ba?, Umman da Kawu ne ya yi hanyar shigowarta? Umman da Kawu yace babar ma'aikaciyar fadarsa ce ya ba Anna a lokacin da take da bukatar taimako sanadiyar haihuwar yaya ciwo ya sameta? Ko kin manta dai?" A hankali NADIRAH ta lumshe idannuwanta, ba komai ke dukan nutsuwarta ba irin tafiya da karya a gaban wa'inda take ji a zuciyarta, ko a da abinda ya saka ta tsani karya dan ta riga ta gane karya abu ne mai zubar da mutunci, zama da mutane kana masu boye boye kuwa munafurci ne, ta tsani halayan nan shi yasa ta iya zama da kowa a rayuwarta, a duniya babu abinda zata kwatanta yi a yi gagawar kamata a gane karya take yi irin boye boye ko karya "Aunty?" Auta ta fada a sanyaye har tana dan dafata Idannuwanta da suka kada suka yi wani irin luhu luhu ta bude tana kallonta Auta ta sake sanyayar da muryarta ta ce" Dan Allah, kar ki hannani zuwa kin ji?" Hannunta ta damka da dan karfin da ya saka Auta kallon hannayensu, sannan ta kalli Fuskar NADIRAH A hankali NADIRAH ta ce" Yaya kike tunanin zan kasance daya daga cikin wa'inda zasu rabaki da yayanki?" Auta ta dan kureta da ido, hakan ya saka NADIRAH yin dan murmushi tana aro jarumta ta ce" Kin san me?, Ni zan so ace inada dan uwanma a duniya, gaskiya da sai na fi kowa jin dadi, dan Allah zaki zamto yar uwa a wajena?" Da wani mamakin Auta ta sake kureta da duba, duba irin na son saka shaku a kan wacece ita? A sanninta Bahija tanad yan uwa maza sosai, ita dai ce daya tak mace a cikin gidansu, sai kuma ta ringa cewa ta so ace ta samu dan uwa? Ko dai yar uwa mace take nufi? Dan jan numfashi ta yi ta ce" Aunty, ki ce kema irina ce, nakan cewa Abahna na so ace inada sister mace nima" NADIRAH ta yi shiru da furucinta tana kallon fuskarta A hankali ta mike ta ce" Tashi mu tafi" Auta ta mike, sai kuma ta tsaya ta dubi hanyar sama a hankali ta ce" Kin hakura Aunty Husnah ta kwana yau ?" NADIRAH ta daga kanta itama ta zubawa hanyar ido, dan tsai ta yi tana kallon hanyar, da sauri ta kade komai a idannuwanta ta juya ta fara tafiyar tana fadin" Auta na kula ke kam baki da gagawa, bara na yi tafiyata tunda ba zaki je ba" Da sauri ta daga kafarta ta bita suka nufi bangaren NADIRAH tare A lokacin da HUZNAH ta kama kofar dakinsa ta bude yannayin hankalinta a tashe, idannuwanta har bata gani da kyau ta yi salama ciki ciki sannan ta shiga lalubar inda yake a idannuwanta Hango shi da ta yi a saman ni'imataciyar shinfidarsa ta farin zannin gado karkar ya sakata nufa jikinta na rage karfi wajen nuna bacin ran da tashin hankalin har ta karasa inda yake kwoncen a hankali ta zuba masa ido, yannayinsa har zuwa rigar dake jikinsa da irin lumshe idannuwan da ya yi wanda ya nuna mata cewa idannuwansa biyu ba barci yake yi ba Jiki a sabule ta duka a gaban bed din, ta yada zata iya dubansa da kyau sannan zata iya dora kanta a saman cikinsa Kanta ta dora a saman cikin nasa sannan ta kawo hannunta wajen fuskarta a hankali ta shiga tare hawayen da ya ki tsaya mata wanda ya bale mata ne sakamakon ciwo da magangannun NADIRAH suka yi mata Muryarta a raunane, sannan a sanyaye , cike da kwontar da kai ta ce" Dan Allah kar ka yarda haka ta faru da ni, dan Allah kar ka bari haka ta sameni SULTAN" Idannuwansa dake lumshe ne suka dan motsa, alamun muryarta na zuwa cikin kunnensa, haka kuma yannayin muryar ya fara damunsa alamu na ya fara jin kamar zai dago daga duniyar tunanin da ya afka "Ka ga, ni kaine duniyata, ba kuma zan iya hadaka da kowace duniya ba, haka kuma ba zan iya kyaleta ta kwace mun kai ba koda kuwa yar uwarka take, ai nima matarka ce ko?" Ta sake fada wannan karron hawayen nata ya yi karfi sosai har ya fara jike rigarsa kadan irin digon da yake yi ya taba fatar cikinsa har ya ji sanyinsa sakamakon sanyin ACn da ya yi kaukau a dakin A hankali ya dora lalausan hannunsa saman alkyabar dake kanta, A hankali ya janye rufar alkyabar ya karasa saman daurin dake kanta shima ya ture shi a hankali sannan ya dora hannunsa saman gashin kanta yana dan shafawa a hankali a hankali sannan ya gangaro wajen idannuwanta ya dan shafo dan ya gasgata kuka take yi? Me ya saka ta kuka ne? Jin lemar ya saka shi dan dakatawa, sannan ya saka hannayensa bayan ya dan dago ya dagota daga duken da take ya haurota sama har ta haye saman ruwan cikinsa yana janye alkyabarta gaba daya ya yarr yana jin ta zamto takura a tsakaninsu A hankali ya dan bude bakinsa kasa kasa ya ce" Menene? Me yake damunki?" Hanci ta ringa ja tana ta kallon fuskarsa da yannayinsa, kanshin turarensa kuwa hadi da na wuta wanda take ji idan matarsa ta gifta ta gefenta take shafa a jikin fatar wuyansa, a hankali ta lumshe idannuwanta hawayenta na sake barkewa Muryarta a raunane ta ce" Yaushema ta shigo da har zata ce ta soke zamana a gefenka idan ranar girkinta ce? Wai a barta ta mori amarcinta? Yaya zata ringa magana kamar ta fini sannin waye mijina?............. Har cewa ta yyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyyy" Zazafan harshensa, mai hadi da ni'imtacen kanshi, da dumin bakinsa ya sakata hadiye maganar a cikin cikinta a lokacin da ya rike lebenta na kasa a hankali yana bude jajayen idannuwansa ya sauke a saman fuskar tata....... A hankali ta ringa kallonsa, a lokacin da ya shiga bata a aikace cewa ya iya wasanin nan da take hasaso yadda zata koya masa dalla dalla har fiye da tunaninta , a lokacin da SULTAN dinta ya dawo mata wani gagarumin bijimin zaki mai yinwarta ya ringa kai dukkan abinda take ji a labarun dandali yana aikata mata a aikace Idannuwanta ta ki kiftawa dan kar aje ta kifta ta ga mafarki take yi, A hankali ta ringa jan numfashi tana sake kallon Mijinta tamkar zata summa dan dadi a yau itama yan jikinta a matsayinta na mace cikakkiya ba wannan dakatar da ita din balle ya koreta A yau ita ke jin gabanta na faduwa na idan ya zo shigan fa abinda ya saba faruwa ya faru da su?, Itace ta rikice ta rasa yaya zata tuna masa halin da suke shiga idan ya kasa samun nutsuwa, tsoro ya gama cikata mai karfin gaske a lokacin da take ta gannin yannayinsa kara rikicewa yake yi, bata taba ganninsa a haka ba, bata taba ganninsa da karfi hankalinsa kwonce zai antaya mata irin na yau ba Muryarta a raunane take ta riko dim diman damarsunnn hannayensa tana kallon fuskarsa mai dauke da ni'imtacen saje baki sidik tana son ankarar da shi lalurarsu. Lokacin da ya kama pant dinta kwalin kwal da ya rage a jikinta ya janye shi ya rabata da shi yana shafa jikinta idannuwansa lumshe kunnayenta suka ringa jiyo zazakar muryarsa yana adu'ar saduwa da iyali idannuwanta a waje gaba daya tana kallonsa har ya yarda ya fitar da abinda sam baya bari ta gani ido bude dan yakan ce cikar banza ne abinda ke sacewa kamar ball idan an sace mata iska du idan zai amfani iyalinsa?, A yau gashi a hannunsa hankali kwonce yana ta kokarin lalama mata dan amsar budurcinta ya nufo da karfin gwuiwarsa ya nemi shiga, sai dai abinda suka gani gaba dayansu ya saka su jin juwa , domin tamkar an saka abin sace abu an sace masa halitar dake hobbara dan tauri da cika ta koma ta yakune tamkar ta tsumma Idannuwanta ta rintse, jikinta na daukan rawa a lokacin da ta ga jikin nasa yake kallo, ga nata jikin a bayane a gabansa hannayensa a jikin cinyoyinta , a hankali ta barke da kukan da bata san dalilin fitowarsa ba, wanda ya fito daga cikin zuciyarta sannan bashi da amo mai karfin da zai saka yan waje su jiyo su, haka kuma tana ambaton sunnan ALLAH ne kirjinta na dokawa da karfi da karfi Tabbas sai a yanzu ya dawo hayacinsa, lokaci daya kuma maganar SHEIK ta dawo masa a lokacin da yake ce masa idan fa abin a jikin HUZNAH yake ne ake ta neman magani ana bashi shi kadai ita kuma ana gannin ai ba a jikinta yake ba?, Sautin muryar kukanta ya saka shi sassauta rikon da ya yiwa cinyoyinta , cike da tausayin iyalinsa ya mayar da gajeran wandonsa da kyar ya iya cira kafar tasa ya haura saman gadon ya janyo abin rufa ya rufa masu a jikinsu sannan ya janyota jikinsa sosai ya rungumeta yana sake lumshe idannuwansa muryarsa a raunane cen kurya ya ce" HUZNAH, ki daina kukan kin ji? Ki yi hakuri plz" HUZNAH cike da tsoro da fara tunanin to wai ko dai itace mai matsalar nan ta ringa rage kukanta har ta dauke kukan gaba daya sannan ta rukunkumeshi a jikinta tana cusa hancinta a kirjinsa tana dan girgiza kanta cike da tunani kala kala, sai dai yau da sauki take ji sanadiyar ganin har gata a jikinsa a haka ya rungumeta har yana bata hakuri, tabbas bata da ja mijinta ba zai bari a wulakanta ta ba komai wuya!, Matarsa kuwa ta zo ta ga karshen zama a gefen mijinsu, uwa uba gata a jikinsa a ranar kwanan nata ta yi abinda take ikirrin zata yi a gani! (😁)............................. Tsaf ta fito daga bayin dakinsa bayan ta yi wanka har ta dauro alwallar sallar asubahi sakamakon kiran da aka yi ta fito a hankali ta rufo bayin ta nemi ficewa dan bi ta boyayiyar hanya ta karasa bangarenta dan a tunaninta tuni UMUGHLUK ITIBEL ya jima a masalaci, domin da ta motsa a barcin ta tabbata shima ya tashi daga barcin ya shige wani Bayin Saman gadon ta kai kallonta da shaukin farin cikin kwananta a samansa yau a cikin jikin mijinta, Kara kurawa gadon ido ta yi, gannin tabas ba abin rufar bane a sama shi ne ya sakata nufa da dan sauri ta hau a hankali ta saka hannunta ta yaye rufar ta kai hannunta da nufin tashinsa, sai dai zafin da ta ji a jikinsa ya saka gabanta yankewa ya fadi da karfin gaske , a tsorace ta dan shiga ambatonsa da sunayen da take kiransa da su irin na girmamawa tana tambayarsa bashi da lafiya ne? Me yake damunsa ne?, Gaba daya hankalinta tashe tana neman fashewa da kuka Idannuwansa da ya kasa dagawa dan zafin ciwo yake ta motsawa , sai kuma ya samu da kyar ya kamo hannunta ya kai wajen da har ya dan kumburar masa dan azaba yana neman kashe shi Duka kirjinta yake yi, da sauri ta haura ta shige ciki, a matsayinta na mace wace ta san kanta daidai gwargwadon iyawarta ta shiga bashi taimako dan gannin ya samu sasauci cike da kula da tausayi da tarin soyaya ko zai iya fita masalaci, sai dai abin ya ci tura, domin tun tana yi da karfinta har kanta ya kage hannayenta suka yi sanyi ya kasa samun nutsuwar da ake lalube, hasalima yannayin bashi da alamun sadakawa sai dai sake yin kiri kiri Muryarsa a jigace , cen ciki ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣7️⃣ Muryarsa a jigace ya ce" HUZNAH???" Dagowa ta yi tana talabe kanta da ya kage tana kallon yannayinsa cike da tausayi, muryarta a sanyaye ta ce" Yaya zan maka ka samu nutsuwa ne?" Idannuwansa ya sake rufewa da karfi yana jin kansa kamar zai fashe, muryarsa a tausashe ya ce " Ki je ki yi sallah, kar mu rasa mu dukanmu" Idannuwanta ta lumshe wasu hawayen na sake ziraro mata a hankali ta ce" Yaya zan iya barinka cikin halin nan bayan na san idan ka kara wasu lokutan a haka zaka iya summa?" Jajayen idanuwansa da har jan ya kafe ya fara yin duhun baki ya zuba mata, muryarsa a jigace ya ce " na ce ki je ki yi sallah, idan kin gama ki huta zan tashi nima na shiga wanka" A hankali ta sake shi ta dan matsa tana kallon yadda ya mike a hankali ya ja abu ya rufe jikinsa sannan ya nufi bayi da kyar yana wata irin tafiyar da take tambayar kanta a haka yaya zai iya tafia masalaci? Rufowar bayin ya sakata sauke ajiyar zuciya ta mike jiki a sabule ta nufi wajen alkyabarta ta mayar ta sake juyowa ta kalli bed din sannan ta fice ba tare da ta gyara ba, domin ba su ke gyaran komai ba akoy masu yi (🤔 harda gadon da kika gama baza sirrin nan?) Da kyar ya iya yin wankan sama sama ya dauro alwallah ya fito Sallar kanta da kyar ya iya gabatar da ita, bale idan zai kai sujada sai ya ji kamar mararsa zata fashe biyu, kunnayensa na jiyo masa adu'ar masalaci watau har an gama sallah an yi karatu ana shafa fatiha ana ta yi masa adu'o'in alkhairi Idannuwansa ya lumshe ya kama abu ya mike da kyar ya nufo hanyar fitowa Sauka yake yi ko rawani bashi da shi a kansa, daga shi sai doguwar rigarsa da wandonta sai carbin dake rataye a jikin yan yatsunsa ya ringa sauka a hankali har ya saukowa hankali kwonce ya nufi boyayiyar hanyar falonsa ya bude ya shiga ratsawa yana dubawa har ya karasa kofar nata falon sannan ya dora yatsarsa wajen budewar ya cire lock din ya murda abin budewar ya dan bude shi kafin ya dakata ya shiga dan bubugawa yana sake jinginar da bayansa da garun Daga cikin falon kuwa, zaune suke Auta na kallon yadda Inna ke yiwa NADIRAH gyaran kai, bayan sun gama sallar asubahin Innar ce da kanta ta je ta dora masu abin kari sai kuma tace su zauna a falo su sha hirarsu, sai daria take sha idan Innar ta yi magana, tana matukar son sannin wacece innar? Ama ta kasa tambaya, hasalima tun jiya da suka karaso bangaren nan suka dan taba hira da ta so tafia fakat NADIRAH tace ba inda zata je ta yi zamanta a bangarenta yaya zata iya yin barci ita kadai a nata bangaren bata jin kadaita ne?, Ta daina kadaice kanta ita kadai ba kyau, sai gashi ta kwonta daki daya da wannan mata Inna sun sha hira da kayan dariya kafin su yi barci, asubahi na tashi kuma ta tasheta suka yi sallah suka taba karatu sannan suka fito dan dora abin kari, domin yanzu haske har ya fan fara fitowa kadan kadan, gaba daya jinta take wani iri, wani banbarakwai, ta gaza sakewa ta sha hira da dariya ne dan wannan lamarin kam bako yake a rayuwarta Sake bugawar da aka yi a hankali ya saka su juyawa su biyun Juyo da kan nata Inna ta yi ta hanyar jan gashin hakan ya saka Nadirah furta" Wayo kaina innata" Inna ta ce" Ke dilla juyo, ana maka kitso kana kauce kaucen kai da iya iskanci, ke ba za'a taba maku kanki ba ko?, To sai na caje maki" "Innata kamar ana buga wancen hanyar fa, dama a bude take?" NADIRAH ta fada tana dago kanta ta kalli innarta Auta kuwa da sauri ta mike tsaye tana kallon hanyar ta ce" Dama wani na iya bude kofar cen banda Abahna?, Idan a rufe take da ky ta ciki Abahna kadai ke iya budewa da yatsarsa kar aje wani abu ke faruwa a masarautar?" Inna da sauri ta mike tana daura zanninta a saman cikinta ta kalli hanyar sai kuma ta kalli Auta ta ce" Yar nan ban gane wani abu na faruwa ba? Abu irin na a tardomu a kashemu?" Auta ta yi tsuru tsuru, hakama Innar NADIRAH Nadirah ta kalli Auta ta kalli innarta itama tana jin hankalinta na neman tashi Zata yi magana ya dan miko hannunsa kadan ya rike abin kamawar ta ciki kadan sannan ya janye, hakan ya saka Auta zarro idannuwanta ta ce" Abahna ne" Gaban NADIRAH sai da ya kwonci kwonci ya rufto kasa, innarta kuwa ta dake kallon Auta ta ce" Makashin? Waye Abanki wai? Ki bude baki mana kina magana a kuryar makogwaro" "Inna wai ASADEEK take nufi" NADIRAH ta fada muryarya a sanyaye sosai Innarta ta zarro ido, sai kuma ta kame baki ta karasa kusan NADIRAH ta rankwasa mata dankwashi kasa kasa ta ce" Dan ubanki ban hannaki kama sunnan nan ba?, Kina nufin shine a cen?" NADIRAH ta dora hannunta saman kanta ta kwashashabe fuska ta gyada kanta Innarta ta tafa hannu ta duke kasa da hannunta ta tura NADIRAH kasa kasa ta ce" Jeki jeki yi maza jeki" NADIRAH ta turo baki tana kallon innarta ta ce" Ni kuma Innata?" Innarta ta sake dora hannunta a gefen fuskarta tana salalami kasa kasa sosai ta dubi Auta da abu biyu suka tsaye mata a rai, muguwar dariya da kuma tunanin me yake damun yayanta? Dama yana zuwa nan da kansa ne?, Ta ce" Ke kin ga wani bakon islanci ko? Tambaya take yi wa zai je, ce nai mata ni, nace ni Indi, in baki je wajen cen kika ji me Babanmu ke so ba sai na ci abinda habu baya so ina fada a gidan nan !" Da sauri ta nufi hanyar tana matsar kwallah, ta karasa ta bude tana leka shi suka yi ido hudu da junna, fuskarsa ta zama jajajir, yannayinsa ya zama abin tsoro, lebensa kuwa ya karra yin ja yana walwali , idannuwansa kuwa sam badu da dadin kallo A hankali ta kalli hannunsa da ya miko mata yana karra shanye dubansa , hannun ya karra girma fiye da da, yannayinsa ya taurara sosai a idannuwanta, jijiyoyinsa sun yi birde birde, sai ta ga ya karra yi mata girma fiye da jiya da dare Da sauri ta juya da nufin guduwa, dan sam sai ta ji wannan yannayi kamar za'a zalinceta ne Dan dagowa ya yi ya damko bulememen hijabinta ya yi baya da ita, a dole ta dawo ta daki kirjinsa har sai da ta ji tsoro domin buguwa ta yi sosai a bayansa , hakan ya sa ta dago da sauri ta juyo ta dago dubanta tana kallonsa, muryarta na rarabuwa ta ce " Me, me yake faruwa? Me yake damunka?" Janyota ya sake yi jikinsa, a hankali ya rungumeta sosai a jikinsa, kanta dake bude an kame gefe, gefen a barbaje yana fitar da kanshi man kai na mata ya ringa sinsinawa a hankali, a hankali , sai kuma ya saketa ya dago fuskarta yana kallo irin yadda fuskar tata gaba daya ta fara daukan ja alamun tsoro take ji ko kinsa take ne oho Tana jikinsa ya shiga nufar nasa bangaren da ita, du yadda ta saki jikinta yake tafe da ita dan ya saketa watau ta ki taka kaffafuwanta dan ya barta kar ya tafi da ita sai ta ji idan ya daga kafarsa du irin yadda jikinsa ke mace da ita yake dagawa har ya karasa kofarsa ya bude ya shiga da ita sannan ta ga ya dora yatsarsa a kai watau ya yi block din kofar har sai idan shine ya bude da kansa , dama babar kofa ba za'a budeta ba sai idan ya bada damar haka, sai ta ji hankalinta ya fara tashi har ta fara yi masa tambayar me ta zo yi ne? Kitso fa ake yi mata, kar a ga bata dawo ba Idan ya tankata tabas dakinma ya tankata, a haka har ya karasa dayan dakinsa da ita ya bude ya shiga ya mayar da kofar ya rufe Tsaye take tana kallon wajen kofar har haske ya mamaye dakin Da sauri ta ringa kallon yannayin dakin sai kuma ta juyo inda yake dan ce masa dan Allah ya bude mata mana ta tafi Idannuwanta ta wara tana kallonsa cike da faduwar gaba Da sauri ta sada kanta, watau ta sada dubanta tana jin kamar zata summe a wajen Idannuwansa ya lumshe a hankali ya yi murmushi yana kallon yannayinta, kasa kasa ya ce " Ba zaki kalleni ba?" Cike da matsananciyar kunya ta kasa koda daga kan bale ta iya bashi amsa, a hakan dan bashi da riga ne, domin da wandonsa a jikinsa A sanyaye ya shiga gabatar mata da kansa, ba da tsawalawa ba, ba kuma da fin karfi ba, sai dai idan da ace zata iya dago kanta ta dube shi ido cikin ido da ta gane a halin da yake ciki yana iya hadiyeta danya Muryarta da nauyi ta ce" Dan Allah kar ka ringa sabawa da ni......., Ka daina tabani ka ji?" Sake kure fuskarta ya yi da kallo, har sai da ta ji shirun ya yi yawa ta dan dago dan gannin ko ya daina matsota har ya kawwota kusa da bed din ne? Tana sauke idannuwanta cikin nasa gabanta na bugawa shi kuma a lokacin ya hade bakinsa da nata damatsunnan hannayensa har motsi suke yi su kadai A yauma NADIRAH ta ga yaren Kato, yare marar taushi , domin taushin na dan lokaci ne a matsayinta na farin shiga, sai dai shima farin shigar ne, idan ya fara burinsa ya samu nutsuwar da yake so A lokacin da ta ga da gaske yake ya zo gadan gadan zai sake ratsata da abin da take kira tabarya dan firgita ta dago a gigice tana kallon fuskarsa da tata fuskar mai dauke da hawaye shabe shabe muryarta a raunane ta ce" Kar ka yi, dan Allah kar ka yi, ba ni bace *BAHIJA*, ni sunnana *NADIRAH*, kar ka kuma buda ni na rasa amsar da zan ba *AMINU*, dan Allah kar ka min....................." A lokacin ta gane ita din shashasha ce, sannan tana iya jan abinda za'a kasheta muttttt har kiyama, domin a nutse ya mayar da ita baya ya kwontar da ita ya warata ta yadda bata tunanu sannan ya antaya mata tashin hankalin a kayan kaniyal ( kashhh maman jariri Allah ya shiryeki ), ta yadda sai da ta ja sheda mai karra sannan ta yi lakwasss tana kallon ikon Allah da jiran mai zare ran ya zare, fatanta Allah ya sa yar aljana ce ita Hakarta ya yi tamkar rijiya, sai da ya jijigeta iya jijiga sannan ya sakar mata rikicin a cikin jikinta ta yadda wannan lokacinma ta ji kamar zai rabata biyu dan azaba Ya jima a jikinta yana rike da ita a cikin jikinsa , yannayi mai girman gaske dake bijiro masa daga cen kasan zuciyarsa mai zafin da bai taba ji ba yake ji yana hadasa masa gumi mai zafin gaske, bai san dalilin da ya saka sunnan nan mai daraja ke son zame masa kamar sunnan makashinsa a zuciyarsa ba, me zata cema AMINU? Sarawar da kansa ya yi ya saka shi dan sake riketa a jikinsa, Kamshi take yi jama'a, jikinta dumi yake fitarwa, idan ya riketa a jikinsa kuma laushin jikinta, taushin jikinta, komai nata kan saka shi jin kamar su dawama a haka, a hankali ya dan sasauta mata rikon da ya yi mata yana kallon fuskar tata, sai kuma ya saketa kadan ya dan mike yana zare jikinsa a nata ya zauna bakin gadon bayan ya ja hijabinta ya raba a jikinsa Tana kukan iya shege ta kama da kyar tana juyawa tana jin zafi ta ja rigar barcin dake jikinta ta mayar jikinta jiki a sabule ta ziro kaffafuwanta sai kukan iya shegen take yi ta mike da kyar ta yi duku duku ta sake dukewa ta shiga kama abu tana dan tafia a hankali da nufin tafiya haka dinta bangarenta ta labe ta ji muryarsa a kausashe ya ce" WANENE *AMINU?*" Bata san lokacin da ta mike tsaye daga dukewar fa take yi ba tana jin jikin nata na yi mata zutzutzutzut ta zuba masa ido tana tunanin Aminu kuma? Waye ya masa maganar Aminu shi kuma? Muryarta a raunane ta ce" Aminu kuma?" Yana kallonta, nasa kirjin na dokawa shima ya mike har sai da hijab din ya sauka daga jikinsa ya kamo ya dan daura shi iya kugunsa ta yadda ba zai yi sallah ba kuma sai an wanke ya nufota gabanta na sake bugawa hankalinta gaba daya na neman tashi ya tsaya a kanta ta yadda gaba daya ya rufe ganin nata har ta yi baya baya zata kifa Hannunsa daya ya saka ya tarota a jikinsa yana kallonta a hankali ya ce" NADIRAH, wanene AMINU?" yanzun kam kuka ta fashe da shi har tana wani far far far da idannuwanta tana neman kifewa irin zata summe din nan muryarta cikin kuka ta ce" NADIRAH kuma? Wace NADIRAH jama'a? Nice Bahija fa?" Cike da jure yannayin bacin ran da yake ciki ya sake juyota yana kallon yadda take wani abu kamar zata summe a dan dake ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣8️⃣ Alhamdulilah na dawo, in sha Allah zamu dora daga inda muka tsaya, ina fata baku manta labarin ba🤣 sannan zaku yi min cmmnt? Godiya nake na nesa da na kusa Allah ya saka da alkhairi Cike da jure bakon yannayin bacin ran da yake ji yana sake game ilahirin jikinsa ya dake juyota ta yada idannuwanta zasu shiga cikin nasa, ya sake riketa ta yadda zata daina zaburar da take kamar sabon kamu, a gajiye ainun da son ganar da ita ya ce" Zuwa yanzu bai dace ace baki gane ba sannin wacece ke ne damuwar ba a wajena, Je te demande une stricte explication !" Ido take kiftawa tana kallonsa, gaba daya da zai sanar mata ko wani kuda ne ya zo masa da sunnanta da bayanin Aminu da ta rage fargabarta a kansa, gashi yana yaren da bata iya ba kwata kwata, ita kam ina zata shiga da ranta yau? Muryarta a sanyaye bayan ta saka idannuwanta cikin nasa da suka yi ja a hankali ta ce" ASADEEK, hausar da ka fada kadai na gane, Dan Allah ka ringa yi min hausa dan ba kaunar wani yaren nake yi ba" Shine ya iya lumshe nasa idannuwan sakamakon abubuwan da zuciyarsa ke ta sasaka masa Ikon Allah, ashe hargitsi na iya samunsa mai duka zuciya wanda bai shafi talakawansa ba ko hakin Gimbiya? Ashe wata damuwa na iya shiga zuciyarsa wace yake son sani ido rufe fiye da damuwar dake damun Auta?, Ashe zai tsaya kerere da daurin gyauto irin na mata a kugunsa yana jiran yar tatsitsiya ta bashi amsa ama su ringa tarere sunna ja in ja? Ashe zai riski irin ranar nan da yana kallo a ambatar masa wani namijin bayan ya gama gane shima namijin ne, wadataciyar bulalar da Allah ya haliceshi da ita tsaf take iyo ta gigita kowace irin rijiya ce? Ashe zai bude kaya sababi ya saka a matsayin na aro? Wacece ita yarinyar nan ne? Me take tafe da shi matsayin aikin da aka bata ta aikata a kansa? Bakinta ya fada, a cikin firgicinta ta zayane, yanzu da ta dawo hankalinta ta karyata! "Hum" ya furta daga ciki ciki, sannan ya saki hannunta ya ringa matsota tana matsawa jikin garu har suka dangane da garun tana jin abinda aka gama wanka mata na bin kafarta kamar makeken ruwan fitsari A hankali ya dake kure fuskarta da kallo A matsayinsa na alkali, ja gaban talakawa ya lakanci sirrin da mutane da yawa basu lakanta ba, a matsayinsa na Uba wa baba da yaro ya lakanci furuci irin na fuskar bawa, wanda yake da gaskiya da wanda bashi da shi Idan ya kalli fuskarta a yanzu kwarai yana karantar rashin gaskiya, sai dai ya fi karantar gaskiyarta a kan rashin gaskiyar, hakan sai ya raba masa abin gida biyu, ta yiwu ita din lwarariya ce wajen iya aikinta na mugun nufi ya sa aka turota, ko kuma gaskiyar da Allah ya haliceta da ita ke son hayowa ta bayanar da kanta? Lebensa ya lashe a hankali yana sake tabatar da abinda zuciyarsa ke wakawa cewa koma mecece ita a haka ya fito dan yakarta, babu abinda ya shafe shi da tarin rikicin dake tare da ita, rikici yau ya fara gani ne? Shi kam a yanzu itace abokiyar gabarsa ita kadai, domin ta hayo ta hanyar da baya tunanin in har zai iya kawar da kai, kau anya kuwa zai iya? Ita wannan ta kama masa wani sunnan daban a gabansa? Aa wannan ba wasan da zai dauka bane! A nutse ya yi mata daukan jariri, daukan da bata zata shi zai yi mata ba, gaba dayama irin tsayuwar yar Indi ta neman hanyar zabgawa a dubun lamba ce dan ta tsiratar da kanta ta kuma kaima innarta rahoton an samu wani shege mai shegen baki ya kaima ASADEEK bayani dala dala dan haka su shirya cire kai a cikin fada dan a yadda ake maganarsa sam ba adalci a lamarinsa, daga ka dan aikata laifi sai ya sare kanka? Ai ba tausayima kwata kwata a lamarin! Da suturun dake jikinsu ya tsaya a kasan shower irin ta zamani wace ke zubowa dan kankin kanta dan aljanci irin na nasara Ta ko'ina ruwan ya ringa sauka a jikinsu, hakan ya sakata tsorata har ta saka hannayanta dake rike da hijabinta wanda ta gama tunanin wannan kuma ba zai yi sallah ba dan ya ga uwawun maza domin da shine ya yi tawul ta hanyar daurawa a kugunsa, ta rukunkume shi sannan ta cusa kanta a cikin kirjinsa muryarta a raunane ta ja sheda tana buda bakinta dan yin numfashi ta bakin Ita kam ta ga abu, a haka a jikinsa ta ringa jin hannunsa mai laushin balaki yana kamar shafata kamar kuma yana dan wanke mata wani abu, gaba daya sai ta sarewa duniya domin wani abu ya fado mata a rai ita da kawarta Yar dubu, a cen kauyen LABA akoy wata kawarsu da aka yiwa auren dole, a dandali suka ringa jin wani bayani wai mijinta manau makaleta ne, bata da hutu ya mayar da ita kamar sutura wace mutun dai mai hankali ba zai fito babu ba, tsegume tsegumen ke yawo a kauye har ta je da maganar gaban Innarta, a ranar innarta ta bige mata baki sannan ta ringa salalami tana shela gudu bayi da balbalin gida tana tambayar shin ta dan me ake nufi ne? Kai karshe dai a rikicewar innarta ita ta zauna ta zayane mata me ake nufi din sannan ta ringa wasa wuka tana cewa idan ta yarda ta je Aminu ya mata irin haka sai ta yankata sannan ta je lahira walakiri ya fara cin ubanta a kabari kafin ta tarda mai kankatttt din wanda ya haramta, sai gashi itama kamar dai makalematan ne Allah ya kawota wajensa, gaba daya sauraronsa da take yi dan ta gane yarensa ne, nufinsa zai karra ko zai ji tsoron Allah ne ya kyaleta? Wani irin body contact ne yake gabatarwa a tsakaninsu mai wuyar fasara, cikin salama ya darwaye mata abinda ke jikinta sannan ya sauketa kafafuwanta a saman nasa cikin dabara ya ringa kai hannunsa kasanta a hankali duda tana tarewa tana dan kura masa ido kamar ta kama kwarton nan, har sai da ya gamsu da abinda ya daukarwa kansa niya a cikin zuciyarsa Sake mayar da ita hannunsa ya yi ya dawo falon nanda jikakiyar rigarta ya shinfideta a saman gadon nan ya zamto sanyin AC ya shiga ratsa dukan kofofin fatar jikinta a dole ta ringa jin wani irin tsigar jikinta na mimikewa sakamakon sanyin, dan haka ya ringa dan son kamo abinda zata rufa cen kasan makoshinta ta furta "Sanyiiiiiiiiiiiiiii" Kallonta da yake yi ya saka shi gane eh sanyin take ji, irin mimikewar da take yi kuwa ya saka shi gane kwarai ba zata yi masa gardama a yanzu ba, dan haka cikin nutsuwa da dane kokowarta a farkon farawarsa ya samu ya daneta kadan har ya dangana lalausan lebunansa a wajen bayan ya bude kafafuwanta sosai ya shiga gabatar mata da mugun sabo, sabon da ba kowani namiji ke yi ba, sabon da idan ka dandanawa mace shi ko ta bariki ko halalinka da wahala ta iya yin nesa da kai, zaka ji ana cewa me yake bata ta nacewa dan banza yana mata wulakanci☹️, mahaukacin sabo ne da namiji ke yiwa mace mai wuyar fasara, wasu matan saboda rashinsama ya saka basa gane kan abin, wasun kuwa sam basa sonshi😁, da wannan ASADEEK ya yi mata wani irin riko, tun tana zarro ido bata gane me yake faruwa har gaba daya ta rikice ta rukunkume fillo tana neman kurma ihu, a rikice ta saki abinda yake so ya sakin watau ta samu nutsuwa ta wannan hanyar sannan zufa ta tsatsafo mata a gaban goshinta dan rikicewa da bakon al'amarin da bata san shi kuma a wani mataki zata ajiye shi ba, A hankali ya haye ya janyota jikinsa sannan ya ja masu bargo ya lulube su da shi ta yadda ta shige jikin nasa ta ringa sauke ajiyar zuciya kamar ta yi gudun tseratar da rai, Hannunta na dama da ta dora a saman damtsen hannunsa ta jimke sannan ta kifa kanta a kirjinsa da irin dokawar da zuciyarta ke yi ya saka shi sauke ajiyar zuciya da yin dan murmushi a saman lebensa ya zagayo hannunsa ya lumshe idannuwansa dan yin barci yana sake jin amon sansanyar muryarta da ta kama sunnansa cirat tana kallonsa hira ce take yi masa kamar na sako da sako............................................................................................. Gishiri gishirin dake saman lebensa yake dan lashewa a hankali yana mai fatan Allah ya bashi ikon gannin ya iya jure wannan aiki, kar aje maimakun ya ci karfinta ya hadasawa kansa da ciwo mai zafi bayan ya rabu da shi. _________________________________ Faduwar Mancheste din da yake kokarin balawa a hannun rigarsa bayan ya gama shiryawa da nada rawaninsa sasauke ya farkar da ita daga nanauyan barcin da ya kwasheta Dishi dishi ta ringa gani kafin a hankali idannuwanta su washe ta sauke dubanta a bayansa Tun daga saman kansa wajen rawaninsa har zuwa kasan wandonsa na shada fara lalausa da kuma farare karkar din kafafuwansa take kallo harda dan sake talabe kanta tana kallonsa a zuwan bai san tana yi ba domin a tunaninta bai san ta farka ba Cikin nutsuwa ya gama dukkan abinda zai yi ya saka farar safarsa sannan ya juyo, hakan ya sakata rufe idannuwanta ruff tana sauraron takunsa da kunnayenta Murmushi ya saki ya karasa bakin gadon ya rage tsayinsa ya mana mata kiss a goshinta, cen cikin makoshinsa ya ce" Zan yi tafia, ki min Adu'a idan kin tashi kin ji?, Sannan ki yi wanka fa kar ki mance........." Idannuwan ta sake rufewa rufff hakan ya bashi nishafi sosai har ya zubawa fuskar tata ido, sannan ya mike ya juya ya saka lalausan takalmansa simple ba na gidan sarauta ba domin abinda zai fitar da shi din bai shafi haka ba lokaci daya ya lalubo wayarsa karama yana rufo mata dakin ya shiga dana msg a takaice ya tura kamar haka" Ki turon adireshin gidanku, yau zan kawo maki ziyara " Da hanzari yake takawa har ya karasa wajen motar da aka bude masa ya shiga aka rufo sannan ya dubi sarkin gida cike da dakiya da mulkin murya irin ta sarakai ya ce" Boyayiyar fita ce" Daga haka ya yi shiru ya gyara zamansa yana dan taba zoben azurfar dake hannunsa yana kallon barin da SHEIK yake zaune Sarkin gida na fitowa da hannunsa ya ringa salamar mutane, hakan ya sa kowa ya juya cikin nutsuwa ya bar wajen domin sun sani idan har fitar sirri ce ZAKIN SARAKAI baya bukatar sanarwa a gari da cikin gida, sannan baya bukatar yan rakiya, harta motar da yake shiga idan fitar sirrin ce bata da number masarautar, su hudu abinsu suke fita, daga shi sai SHEIK, sai Direban dake jansu, sai DAN SAWANIN yaki wanda yake tafiye a saman doki komai nisan wajen sannan shi a nesa kadan yake da su bama zaka dauka tafiyarsu daya ba, hasalima shi din abin tsoro ne wa idannuwan al'uma , haka kuma WA'INDA suka san shi idan suka ganshi a waje sai su shiga neman UMUGHLUK ITIBEL dan sun san tafiyarsu daya ce A hankali motarsu ta fara tafia, daidai lokacin da UMMA ta fito daga Bangaren Auta tana ta neme neme da tunanin ina yarinyar ta shiga yau?, Idannuwanta suka sauka a bakon lamarin, bakon lamari mana ASADEEK ne zai fita ba da sanninta ba? Ta san motocinsa na sirri baki dayansu, ko a cikin gari zai yi fitar sirri yakan sanar mata ko ta waya ne, ama a yanzu sai bayan motar ta hango tana ratsa jama'ar fada babu mai kaucewa da dukawa dan babu wanda ya san su waye a ciki bale a gane UMUGHLUK ITIBEL NE ! Gabanta sai da ya kwonci kwonci ya fadi dan haka kawai ta ji hankalinta na neman tashi da gannin haka Da sauri ta juya ta nufi bangaren................................. 😁mun dawo, zamu dora in sha Allah *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 4️⃣9️⃣ Da sauri ta juya ta nufi bangarenta dan zuwa ta yi kiran numbarsa, saima ta manta da neman inda Auta ta shiga domin gani take yi wannan rikicin ya fi na neman inda mahaukaciyar y'ar nan take Tunda ta shige ta zauna ta shiga kira a karamar wayarta gaban munafukan bayinta WA'INDA bata boye masu komai Kira ta ringa yi har sau uku ama ba'a daga ba, a dole ta dakatar tana hucin dake fitowa daga cen cikin zuciyarta tana kallon waje daya, domin ta sani ba'a masa kira sama da biyuma , idan ka yi daya biyu bai amsa ba ka bari zai taboka da kansa ne Daya daga cikin bayin ta kara sada kanta tana fadin" Allah ya taimaki sarauniyarmu , sannan uwar UMUGHLUK ITIBEL, Allah ya karawa Gimbiyarmu lafiya da nisan kwana, zamaninki dawamame ne Uwa a wajen zaki, sannan mata daya kwal a wajen ja gaban da muke hari, me yake bata ranku haka ne?" Cike da hura hanci take dubansu, a kausashe ta ce" A tsakaninku ku uku, akoy wace ta yi sake da aikin da na sakata ne a cikin gidan nan?, Ina nufin akoy wace bata cika aikinta yadda ya dace ne?" Kusan a tare suke girgiza kawunnansu cike da gaskata mata yadda suka saba yi mata aiki basu cenza ba! A birkice ta ce" Da mamaki kuwa!, A tarihi a kusa kusan nan ASADEEK bai taba yin fita ba tare da na sani ba!, Rabonsa da irin haka tun yakin sakashi jikina da na yi wanda ni kadai na san irin rayukan da na kawar kafin haka ya samu, dan bama so ya waiga ya ga kowa sai ni kwalin kwal, a yanzu kuma gayacen ya fita ko ina ya nufa?" Wace ke yi mata leken bangaren UMUGHLUK din ce ta dauki magana tana fadin" Allah ya taimakeki, ta yiwu wani abin ya diro masa kai tsaye, irin mai dirowar nan ba tare da an shiryawa hakan ba, domin ni dai a jiya ina bangaren nan dan kuwa su Kamilu suka yi gadi ya barni na shiga da shigarkin nan, kuma ina nan ta fito da sasafe tana hawayen da ta saba na zo na sanar maki har muka sha dariyar abin, daga shi babu abinda ya faru hasalima sai da na tabatar ya hau salaya na yi anfani da ky din wajenki na fice da taimakon Kamilun, bayanshi sai fitowarnan tasa da kika ce mu dawo mu jirayeki zaki je da kanki Bangaren Auta dan wannan ta ce maki bata kwana a bangarenta ba" Umma ta sake yin jimmm, sai kuma ta mike ta nufi dakinta ta rufo ta karasa wajen akwatin da ta boye maganin da aka turo dan NADIRAH ta zuba masa a abinci ta dauko tana jujuyawa, Tunda aka kawo maganin ta so a yi anfani da shi, ama Nadirar ta nuna mata ba yanzu ba, wai ta dakata ta gama abinda take yi, kwata kwata bata san me yasa take sauraron yarinyar ba, abinda ta sani shine har wani shayin yarinyar take yi bata iya hawanta kai tsaye, ko dan tana da bakine? Ko idannuwan nan nara masu lulumshewa dake hadasa mata kasala da jin kamar ta janyota da karfi ta auka mata ne?, Akoy dai wani abu mai karfi a tare da yarinyar, ama kuma ta san ko ba komai yarinyar kamar ta san kanta, dan kuwa a irin yadda ta fara shigewa ASADEEK ta tabata zata gabatar da aikinta a kan tsari, dan hakama zata karra bata lokaci kadan ta gani! Tino NADIRAH da ta yi da yannayinta ya hadasa mata bukatar aikata aikin da ya fi komai dadada mata ruhi, hikimar ubangiji kuwa ya bige mata tunanin dake ranta na neman auta harma ta ba bayinta dama suka rufe su hudu a dakin suka shiga aikata masha'arsu! ( Subahanalah) Wani wiki wiki fa ita ta karaso falon bayan ta bude kofar ta shigo ta ja turus tana kallonsu kamar yadda suke kallonta Auta kam tsam ta yi tana karewa NADIRAH kallo, kasancewar cikin bargo ta yi barci suturarta a jike ya da ba wani bushewa da kayan suka yi ana gannin jikarsu, kai harta irin laushin da gashinta ya yi ya kwonta lambak zaka fahimci wanke kan ta yi, ga hijabin dake hannunta kasancewar milk color ne ana iya gane jikarsa a ido dan kuwa bata saka shi hasalima kunyarsa take ji a ranta ita kam, da shi fa ya rufe abin jama'a! Innarta kuwa kallon tsaf ta kata sai t dauke kai ta ci gaba da jera girkin fa suka yi ita da Auta ba tare da tace da ita ufan ba, domin alamun yan rikicin sun bayana a tare da y'ar tata, idan kuwa ta biye mata ta tabata zata juye mata borin kunya a kanta ne har ta nada nata duka a banza a wofi, Kai ta juya wajen agogon dakin ta kalla, a zabure ta dake juyowa tana auna irin awanin da ta dauka a cen kennan? Ita da tace a bar kofa a bude ba inda zata? Kai innalilahi wannan wani irin tarin abin kunya ne haka ke yi mata tarere a cikin jama'a? Da yannayin bigicewa tana ta taro kafadar rigar da ba faduwa yake yi ba ta ce" Ina kwana Innata" Innarta ta sake tsareta da ido sai kuma ta dauke kai ta ce" Lafiya, je ki yi wanka ki zo mu ci abinci" Fuskart ta takwakwaba nan da nan sai ga hawaye yana harhada kansa murya na gargada ta ce" Wanka kuma Innata? Me yasa zan yi wanka ni kuma Allah na tuba?, Babu abunda ya hadani da wanka Innata..........." Ta karashe tana sakin hawayen harda jan hanci fuska kuwa ta yi mata jajajir tana kallon innar tata Hindu ta ajiye kwanon dake hannunta tana tafa hannu ta ce" Indi idan baki yi aniya da saurin kukan nan ba ina mai tabattar maki idan na kama kifa maki mari ko Habu ba zai amsheki ba bale Aban birni, da kaniya kin yi wanka da safe ne? Yau ga ya yanzu kuma wankan ne zai zama rigima? Wuce malama maza ki je ki yi wanka na sabulu tas ki yi kwaliya ki fito mu debi girkin nan idan kuma kika jima a ciki in bamu cinye kazar ba ki ce min ba Hindun habu ba!" Ido ta kikifta harda su sauke ajiyar zuciya jin wankan ashe na sabulu innarta ke nufin ta yi Dakinta ta wuce tana harhada tafia dan har ga Allah ba fa rasss take ba, burinta ta yi wankan nan ta dawo ta sanarwa innarta abinda zai summar da ita, danma kar ta fada yanzu ne innar tace sai sun koma wajensa a haka a ringa mata gani gani? Auta dake tsaye idannuwanta a kan tafiyar NADIRAH suka sauka har ta shige dakinta tana cicin magani irin karma a wani kawo mata maganar da ba ita ba ta rufo a kan idannuwanta A hankali ta dora dubanta a kan Inna dake ta dawainiya da kwanuka sai sake goge su take yi tana dan wake wakenta kasa kasa sosai hankali Kwonce A hankali ta kai zaune saman kujera tana ta fama da tunaninta, har fada take yiwa kanta cewa me kuma ya hadara da irin wannan banzan tunanin? Ai ba huruminta bane sam, sai dai kuma katutun da abinda ta dan ba mai yiwuwa bane ya yi mata a kirjinta ya sakata sada kai ta yi wani iri Inna dake miko mata ruwan Adu'a ta ga bata amsa ba ta ce" Ke kuwa tunanin me kike haka da yarintarki da komai harda wani motsare lebe kamar kina rike da duniyar nan?" A hankali ta Kalli inna, zuwa yanzu ta gama gane Inna da yannayinta, shi yasa take biye da ita kamar jelar kare A sanyaye ta sake kallon hanyar da NADIRAH ta bi muryarta a dan sarke kadan ta yi dan murmushi ta ce" Ko me ya jima auntyna a kafa ne?" Inna ta juyo ta kalleta, sai kuma ta dauke kai ta ci gaba da hade hadenta a cikin nonon rakumin nan ta miko mata sabuwar tatsa ta ce" Dan kafa kai ki shanye wannan ki bani" Auta ta amsa tana kallon yadda nonon ya cenza kalla , tana kallon nonon ta ce" Inna menene a ciki?" Inna ta tabe baki ta ce" Haka fa, ku kam aikin da kuka fi kwarewa a shi kennan, tambaye tambaye baku iya nema ba, sai a riskaku ku ringa yada kai kamar kadagaren da ya sha jifa, Allah na tuba sarauta ko ta makada ana jifa ana shige da fice bale masarautar AGADAZ?, Gashinan ita wancen ai abin inaga a jikinta ne ko? Tunda ai labari dai kasa kasa ana jinsa sai hakuri, ki kafa kai ki shanye ki bani malama maza kuma ki shige ruwan cen da na tara ki yi wankam na zo na maki turare du kin zama wata sangayayiya kina tafe kamar baki da laka a jikinki, ni ba zan yarda da wannan iya shegen ba, ku zagine ku amshi gyara da nemam tsari ba iya kwaliyar da takun kasaitar ba kina raye makashinki a tare da ke, kuma abinda kike tunanin a kan Indi da aban datawa hakane , wai ni za'a yiwa magana a rufe jama'a? Ku dai Allah ya shirye ku baki dayan ku!" ....... Sababi Inna ta ci gaba da yi har ta shige Kicin ta shiga hasa wutar da zata yi masu turare turarenta da tace Habu ta tuta ya amso mata ta bar Auta kamar ta summa a tsaye Da sauri ta kafa kai ta shanye madarar sannan ta nufi dakin NADIRAH *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣0️⃣ Nadirah na zaune tana mulka kurkum a jikinta mai hade da madarar gari dan shiga wankan mai gaba daya domin sai da ta kunce kitson da innarta ta mata dan ta wanke kan gaba dayansa ta dago tana janyo hijab dinta a gefe ta yafa a kafadarta tana amsa salamar Auta Zama auta ta yi tana murmushi ta ce" Sannu aunty, ko na rayaki murzawar?" NADIRAH ta yi dan tsai tana kallonta, sai kuma ta girgiza kai ta mika mata dilkar ta juya tana fadin" Murza min a bayana to Auta, dan Allah kar ki darza da karfi jikina gaba daya ciwo yake yi, na san dan na yi sharar bangaren cen ne........." Auta lebenta kawai ta dantse dan gudun dariya kar ta kubce mata, wani irin farin ciki marar misaltuwa take ji yana taso mata, ashe ashe abinda ya faru kennan? Lalle dole yayanta ya zabura da NADIRAH ta fara ihun jinni a hancinta, dole du abinda ta aikata ya ringa binta da ido kamar ya ga bakuwar halita, dole ta siye gaba daya tunaninsa da motsinsa, ya salam wa zata fadawa wannan abin farin cikin? Bata da wanda zata fadawa, sai dai dan godiya ga ubangiji sai ta yi azumi daga gobe in sha Allah, tana gama shafa mata ta yi gaba tana tatare tataren kayan murje murjen ta shige bayi ta rufo bayan ta ce" Kainama sai na wankeshi sai kaikayi yake min" Ita dai Auta sai da ta ga rufowarta ta sake zamaa tana kyakyata dariyar da a kusa kusan nan bata ga abinda ya sakata yinta ba Mikewa ta yi ta bude window din dakin ta lumshe idannuwanta iska mai dadi na hurota, a hankali ta furta" Hakurin bawa keda wahala, da ace bawa zai jure da addu'a ya yi ta hakuri da tabas zai kai ga ci, Allah ka nuna min ranar da zamu rike dan jariri malakinmu a gidan nan..............." Sai kuma hawaye ya bale mata na tarin kauna da tausayin yayanta, harta Huznah sai da ta bata tausayi, shekara nawa tana tare da shi, shekara nawa tana jurewa tana daukan hakuri? Ashe abin a jikinta ne kuma ta yiwu a kansa ne kadai abin, ta yi sake abu ya riketa tunda yarintarta har shekaru sun fara taruwa a kanta, a yanzu idan abin nan ya bayana yaya zata ji a zuciyarta ne? Ga HUZNAH da baban kishi mai tsananin gaske, HUZNAH bata hada mijinta da kowa ba kuma ta so a rabar mata abinta, danma ta san bata da yadda zata yi ne ta hakura da wannan lamari, to ina ga ta ji baban abin nan? Subahanalah lalle akoy kura a baban daki! A cen kasan zuciyarta kuwa dodonta take kamaltawa, tana tinano irin abinda ke iya faruwa, idan ta tuna magangannun Umma a kan yayanta cewa shi da mace sai dau a lahira in ana badawa, shi da samun Da sai dai in ana haihuwa a lahira? Sai ta ji du duniya babu wanda ya yi asara irin mai hada UBANGIN SAMAI DA KASAI DA WANI ABIN HALITA KO GUNKI!, ya Allah ka karra durmiyar da mu a duniyar musulunci😊 ____________________________________ Tabas, dukkan abinda ya dace a tarbi bako dan karama shi, an gabatar a tsaftace a kuma tsare, sai dai bakon nata tunda ya zauna zama irin na hamshakai bai kalli abubuwan ci da sha din ba kwata kwata, hasalima shi ba danna waya yake yi ba bale tace dannar waya ne, shi kuma ba wani abin yake yi daban ba gayanan dai a zaunen ya dake har wani tsoron sake gaishe shi take yi bayan irin ihun da ta sha da ta karanta sakonsa cewar gayanan zuwa gareta? Wayar dakin ta je ta daga, a dake ta ce" FATIME, KI KAWO WANI ABIN WANNAN BAI MASA BA" tana gamawa ta koma ta zauna ta sake zuba masa ido, Shi kuma ci kanki bai ce mata ba yana ta nazartar girman wautarta kafin ya dirar mata An dauki minti kusan goma a haka sai TV dake hasko yan indiya sunna soyaya, Fatime ce ta yi salama yana dauke da wasu plate plate na kwalba masu nauyi da kyan gaskw, kyansu zai sheda maka kudinsu ta kawo ta ajiye ta juya bakin kofar da baiwa ke tsaye tana amsowa tana ajiyewa a gabansa sannan ta duka muryarta a sanyaye kanta a kasa ta ce" Barka da yamaci uwar gijiyata, wadinne zan kwashe a ciki?" Da zafi zafin gannin jimawar Fatime din BAHIJA ta ce" Dillah tashi daga gabansa karki saka ya shaki karnin dati malama kin matse masa waje kina magana daf da shi kamar kin samu talaka dan uwan............................ Dif ta yi shiru sakamakon kakausan kallo, mai hade da tarin mamakin gannin wannan abin rashin da'a a gaban idannuwansa na wannan yarinyar karama tana wulakantar da matar nan da muryarta kadai ya ji ya fahimci ta girmeta ba tare da ya kalli fuskarta ba A hankali ya dawo da dubansa kan FATIME da kanta ke kasa ta rintse ido tana jin kunnar magangannun BAHIJA yar da ta haifi sama da itama ama dan tana aiki a karkashinsu take neman wulakantata har haka? Sake kallon BAHIJA ya yi, sai kuma ya maido dubansa kanta a hankali ya ce" TASHI KI TAFI" Tunda ya zauna sai yanzu bakinsa ya yi magana, hakan ya sa Bahija sake dubansa kirjinta na dokawa, gashi da ta so zama daf da shi kiyawa ya yi ya nuna mata kujerar dake facing dinsa wai a kiyaye shedan Fatimema a hankali ta dago kanta da idannuwanta jin magana a tausashe an yi mata ta sauke kan fuskar mutumen Fuskar ta yiwa tsai na yan sakwani sai kuma ta dauke da sauri sanadiyar gannin ya wani dan warra dubansa a kanta Kai ta sake sadawa a sanyaye ta ce" Allah ya huci zuciyarka, a huta lafiya" Daga haka ta mike ta juya da niyar tafia, Muryarsa ya sake budewa a hankali ya furta" Dakata " Fatime ta dakata, gabanta na tsintsinkewa ta juyo daga inda take ta duka ta ki yarda ta hada ido da shi sakamakon fuskar dake son yi mata yawo a ido wace ta tabata hade hade ne kawai Sake zuba mata ido ya yi kirjinsa na bugawa da dan karfi, sai kuma ya kawar da kansa da hannunsa ya yi alamun tana iya tafia Har ta bar dakin yana kallon hanyar da ta bi ta fita A hankali ya maido dubansa kan BAHIJA dake kallon abunda yake faruwa zuciyarsa na ta ambaton kamanin da ta ganni a fuskar matar nan Murmushin yake ya yi yana sako kalar serius a hade hade ya ce" Haka dama suke jinnin sarautar?, Basu da tausasawa wa mutun?" BAHIJA ta sauke ajiyar zuciya jin ya fara bata hankalinsa ta ce" Kar ka damu da wannnan, baiwata ce ai" "Dama a masarautarku ba'a daina bautar da bayi kamar a zamanin jahiliya ba? Ko bakwa girmama daraja irin ta dan Adam?" Ya fada a sanyaye, fuskarsa na fitar da murmushi, ama kuma bayanansa na suka Kwarai da tana da hankali da tun a nan ta fara gane wani lamari a tatare da zaki, yana magana a wajen da yake nata ne tamkar nasa hankali kwonce yana neman birkita mata lisafi Sai dai murmushin dake saman fuskarsa ya fi komai dauke mata hankali, dan haka ta ringa mayar masa da sakon murmushin itama tana ji a zuciyarta da ace zai amince ta dawo daf da shi da ya taimaka mata fiye da tunaninsa Cikin rashin ba maganar mahinmanci ta ce" Ita wannan din hasalima bata yi min ba, mun cika fada da ita, duda ta min wani dan kokari ta bada yarta auren da nake fada maka ni aka so yiwa shi, ama kwata kwata ba zata taba birgeni ba, bata da aiki sai son yiwa mutun fada kamar itace Gimbiya, a haka da ka ganta ba tsorona take ji ba, tana wani sasada kai tsaf take iya hada ido da ni ta gagaya min magana, abinda ka ga gimbiyama bata tsira ba bale ni?, Ka manta da batunta dan Allah ka sanar min, wai da gaske tafiyar nan tawa ce ni kadai?" 'YA SALAM......., YA SALAM, YA SALAM..............MMMMMMMM.......' yake ta ayannawa a cikin zuciyarsa, da kyar ya iya hadiyewa duda ya dan san lamarin, ama a yanzu da ya ga mahaifiyarta da kamaninta fa irin relation din dake tsakaninsu sai ya fara tunanin anya da son ranta aka yi kuwa? Dan kurmushi ya yi a saman lebensa ya ce" To ita yarinyar itace ke son auren sarkin ko?, Ke bakya so sam?" Cike da jin maganar wata ba ita ba zata dameta ta dage kafadunta ta watsa hannayenta ta ce" Anya kuwa?, Inaga biyaya ta yiwa iyayenta, inma menene cen ta matse mata ta je ta runguma ni kam bana so bana bukata me zan yi da wani bayan gaka?" Kallonta yake yi, ita kuma zuba take yi hankali kwonce har ta dasa aya tana kallonsa ta ji shiru bai ce komai ba kallonta kawai yake yana mamakin asarar mace har mace da aka yi a wajen nan, tap lalle ya tausayawa wanda zai iya kwasar wannan yar idan ta tsira da duniyar!, Ikon Allah yaya zaki ringa magana kina nuna wata biyaya ta yiwa iyayenta bayan ke kin bijire a gaban namijin da kike ikirarin gashi shi kike so ki aura? Uhum Basarwa ya yi yana kallon gefe a lokacin da ta taso tana fadin" Bara na zuba maka jus din plz, ko shine ka dan sha mana?" Jus din ya dan kalla a lokacin da ta zuba harda su rage tsayi tana sakin murmushi hakoran makarta a waje abinta Hannunsa ya saka ya amsa ya gyara zamansa kadan ya dan surba sannan ya ajiye ya sake dubanta a lokacin da take shirin zaunawa tana murmushin gannin ya sha ya ce" To babu tauye haki? Idanfa tana son wannin itama kuma aka yi mata dole?" Yanzu kam ido ta zuba masa tana son karantar asalin menene damuwarsa da maganar nan ne Fisabililahi? Yaya zai zo bayan ta yi doguwar tsumayin ganninsa bayan lokaci mai tsayin nan har ta cire rai ya zo ya ringa fitinar tumaninta da zancen wace bata da wani daraja? Menene a cikima dan an mata auren dole? Da ya san abinda zata aikatama da ya yi mata wa'azin hakan ga dukkan alamu Girairakinsa ya dage yana dan kausasa kallonsa kadan a kanta, hakan ya bata damar jan numfashi tana sauke nata duban domin wani irin kyau da ya karra yi mata tamkar aljani, ita kam ta shiga uku da ranta da soyayar wannan mutumen A sanyyaye ta shiga fadin" Tamkar ba maganana bane a gabanka , tamkar ba nu bace a gabanka, ka duba ka gani ko yaba kwaliyana baka yi ba bayan sai da na kirawo kwarariyar mai kwaliya ta yi min, gaba daya yanzu hankalina ya fara tashi, ina tsoron jin bayani a kan abinda ya shafe mu" Gannin idan ba sake sasautawa ya yi ba ba lalene ya samu dukkan abinda yake son samu ba ya saka shi dan sakin fuskarsa ya ajiye maganar NADIRAH gefe ya dan ringa biyewa shirmenta har ya kara minti biyar ya mike ya yi mata salama Nan hankalinta ya yi mugun tashi, gaba daya ta nemi rikicewa, Gani take yi idan ya tafi ta yiwu sai wata shekarar kuma?, Dan haka a birkicenta ta ringa tambayar sai yaushe kuma? A nutse ya ce" Na zo fa, kuma tafiyarki ce " Wannan kalamau su suka sakata kwonciyar hankali har ta so yi masa rakiya, ama ya nuna sam baya son hakan ta koma gida, a dole ta komawarta shi kuma cike da kamala yake takawa a cikin kebaben gidan da aka kebe NADIRAH har ya kawo baban get din da mai gadi da kuma mahaifin NADIRAH ke zaune sunna dafa shayi sunna dan hirarsu, a dazu baya nak su ASADEEK suka karaso, shi yasa bai ganshi ba sai yanzu Tunda ya yi masu salama bakin mahaifin NADIRAH ya katse da amsa salamar da ya dauko da nufin yi Kallonsa yake kamar ba gobe, har ya zo ya shigewa ganninsa Daga kafar da ya yi ya yi takun sauki har ya karada wajen motarsa nan da nan ya saka mahaifinta farga da binsa da kallo da ya yi Cikin takun sauki ya karasa wajen motar ta barin da SHEIK yake ya kama ya bude kansa tsaye Ido hudun da suka yi da Sheik, da zaburowar da SARKIN yanka ya yi daga maboyarsa haniniyar dokinsa ya fargar da ASADEEK abinda yake shirin yi watau sare hannun wanda ya bude motar da suke ciki ya saka shi saka hannunsa ya bude motar da karfi ya fito gaba dayansa da rawanin da yske shirin daurawa ya taka kafarsa taku biyu ya tarbi gaban SARKIN yanka da yaren buzance ya ce" Basssss! BASSSSSSSS ITBAL!" (JUYA , JUYA SARKI) "UMUGHLUK ITIBEL" MURYAR mahaifin NADIRAH ta furta a lokacin da ya kai gwuiwoyinsa gaba daya ya dire ya sada kansa dan girmama mutumen da koda ba zakin sarakai bane tabas ya ciri tutar amsar gaisuwarsa koda baya so Dif ASADEEK ya yi daga tsayen nan ya kasa juyowa har sai da ya ji kokowa da kuma shirun da ya wakana a wajen sannan ya juyo a hanzarce ya shiga bayan motar ya rufe da kansa ya mayar da kan nasa jikin motar ya jinginar yana lumshe idannuwansa lokaci daya ya damki rawanin ya dafka shi da abin motar muryarsa a bace da amon bacin rai ya shiga fadin" 😩😩😩😩😩😩😩😩🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ Ni fa bana yi weekend fa😩 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣1️⃣ Mun bani an kuma dauke wutar😩😩😩😩 nepa☹️ "shi kuma waye wannan?, Yaya aka yi ya Sanni?, Yaya zai kutso ya katse min binciken abinda ya kawo ni? Bayan dogon hakurin da na yi da wancen marar tarbiyar ya kuma lalatan lokaci? Hakan na nufin sai na kwana a garin nan ko me?, Babu inda zan je idan ban san ainahin abinda ke neman numfashina ba!, Bata isa ta ringa rayuwa da wani a tunaninta ba, bata isa ba!" Fada ne na mamaki, fada ne da duka rasa dalilinsa, hakan ya sa suka yi shiru gaba dayansu babu wanda ya furta koda A ne har suka karasa bakin jejin wani a rakumi ya yi masu ja gaba suka karasa boyayen gidansa na garin TANUT din wanda ke zagaye da dakarun buzaye a saman rakumansu sunna zagaye kowane shirye yake a mutu idan ta kama, dan babu wanda baya dauke da takobi mai kaifin balaki da kuma bindiga ta zamani Fita ya yi ya karasa cikin falon ya zauna ya zubawa waje daya ido kansa na sarawa, lokacin sallah da saura shi yasa ya dakata a nan Ya dauki lokaci a nan a zaune SHEIK ya shigo da salama a bakinsa cikin nutsuwa ya ja ya tsaya har sai da ya budi bakinsa a hankali ya amsa a saman lebensa sannan ya sauke ajiyar zuciya ya karaso ya zauna face da shi A sanyaye ya ce " KISHI?" ASADEEK ya yi tamkar bai ji abinda ya fada ba, har sai da SHEIK ya maimaita kalmar yana kallonsa Fuskarsa da yannayin rikicinta ya dube shi yana kausasa kallonsa ya ce" Me kake nufi da kalmar KISHI?" Sheikh ya sauke dubansa a cikin na ASADEEK, sai kuma ya dan girgiza kansa a hankali ya ce" Bana nufin komai,, gani na yi tunda muka taso yau jinninka yake kan Akaifa" ASADEEK ya juyar da kansa bai ce komai ba Sheikh ya sake sauke ajiyar zuciya a hankali ya ce" Shi din wannan mutumen shine wanda aka barmu a cikin masalacin mu hudu , a gabansa muka tatauna da sarkin garin nan, kuma yana cikin shedun da suka sheda daurin aurenka da ita, haka kuma ba zan manta fitarsa a lokacin ba, ana gama daurin aure ya fice da sauri , da ba dan ba kar nace hawayen me zai fito daga idannuwansa da nace har kamar hawaye na bin kumatunsa, ka ga dai yannayinsa ka san bashi da karfi, kusan shine marar karfi a wajen domin ko a ranar ba wata sutura mai tsada bace a jikinsa, sai dai yana tare da wata boyayiyar nutsuwa da sadadan kallo, a yanzu haka ganeka da ya yi kai ka san akoy wajen da ya sanka, da zaka amince idan ka huta ya shigo mu zauna da shi mu ji ta bakinsa, ta yiwu ya dan wani abu a cikin wannan kulli" Bayan Sheikh ya dire maganarsa ASADEEK ya dauki minti uku a kalla yana sauke ajiyar zuciya yana ta korar abinda ke cizo shi A hankali ya gyara zamansa ya ce" Ban gaji ba, a shigo da shi" Sheikh ya sake kure shi da kallo na yan sekwani, gaba daya da zai ji tashi da ya hakura har ya samu nutsuwar zuciya , sai dai tunda ya kiya babu yadda zai yi , a dole ya mike ya fice ba wani kwarin jiki ya fita dan sanyo bakon Su uku suka shigo, SHEIK a gaba, mahaifin NADIRAH a baya, sai sarkin yanka a baya hannunsa saman takobinsa dake jikin tsatsonta, fuskarsa kuwa sam ba alamun sasauci Sheikh kadai ya zauna saman kujera, Sarkin yanka ya ja ya tsaya ta hanyar wara kafafuwansa rawaninsa na sake rike zagayayiyar fuskarsa, Mahaifin NADIRAH kuwa a kasa ya duka a nesa sosai kansa a kasa ya yi shiru, domin ba'a bashi damar da kawo da gaisuwa bama bale ya kawo din Dan shiru wajen ya dauka har sai da SHEIK ya gama karewa ASADEEK kallo zuciyarsa cike da mamakin rashin hakuri a abinda ya shafeta wanda kiri kiri yake turewa ama bai san a bayane yake a fili bs SHEIK ya dubi bawan Allahn nan da haka kawai yake jin yana iya sauraronsa ya ce" Bismillah, ka yi hakuri ka sanar mana wanene kai? a ina ka san UMUGHLUK ITIBEL?, Yaya aka yi ka gane shi?" Mahaifin NADIRAH ya dago fuskarsa a sanyaye ya kalli SHEIK, sai kuma ya sake mayar da fuskar tasa muryarsa a sanyaye ainun ya ce" Allah ya taimakeka, a gafarceni, tunda na ga ABAN DATAWA a wajen nan hankalina ya gama rugunzuma ya tashi, gaba daya tsoro ya darsu a zuciyata, na tabata tunda na ganshi a wajen nan ya san yarinyar dake gidan ba ainahin ita bace aka .............mmmmm" "Yaya za'a baka umarnin wani abin daban, ka ringa yi mana bayani a kan wani daban!, Ka kama kanka!" Sarkin yanka ya fada a kausashe Hankalin Mahaifin NADIRAH sake tashi ya yi, ya rasa me zai ce yanzu kuma, ko dai rikicewarsa ce ke neman saka shi aikata abinda ba'a nufi cen da shi ba? Kar dai ba abinda yake tunani bane ya kawo su shi kuma ya bude baki yake sanar masu abinda ba'a tambayeshi ba? "Ka barshi ya yi bayanin abinda yake son fada ITBAL!" Muryar ASADEEK da ya dago daga jingine jin kalaman dake bakin wannan bako Dubansa ya maida kan Aba , ya zuba masa ido Ainun, daga irin tsugunnon da Aba ya yi a kasa kaffafuwansa a tankwashe a jikinsa da irin hade hannayensa da ya yi ya saka shi kallon saman cafet din nan a nutse ya ce" Bismillah ka dawo nan ka zauna" Aba ya sake sada kansa, cike da girmamawa ya ce" Allah ya huci zuciyarka, nanma daraja ne a wajena idan har a gabanka nake, a yafe min, a gaffarceni, na aikata kuskuren budar bakina a yi mib afuwa , zan sanar a inda na sanka, sanadiyar iyalina a lokacin da aka so yankewa mahaifiyarta hukuncin kisa, nine nan ka bayar masarautar Tanus cewar na zamto sarkin dawakai a bisa adalcinka da kuma tausayinka, na tabata ka manta kamanina, sunana SALIHU daga kauyen LABBA" ASADEEK ya Sake fuskantarsa, tabas an yi haka da jimawa, asalima a lokacin ba shine zai yi shara'ar ba, mahaifinsa dai ya saka shi ya bashi umarnin zuwa da yanke hukunci yadda ya dace A nutse ya ce" Bayan wannan , me ka sani dangane da maganar BAHIJA" Kansa ya dago, irin duban da ya yi masu babu wanda bai ga tashin hankalin da zuciyyarsa take ciki ba, ya yi hakan ya kai sau uku, ama a cikinsu babu wanda ya fahimci da ace zasu taimaka masa su ce da shi ba sai ya fadi komai ba da sun rufa masa asiri, baban tashin hankalinsa iyalinsa, yaya za'a yi da su? Wani irin hukunci zai hau kansu? Subahanalah yaya za'a yiwa NADIRAH?, Innarta fa? A dole hawaye ya shiga bin gefen kumatunsa Sosai ya karra sada kansa hankalinsa na tashi A sanyaye ya ce" RANAR talata ne, FATIME ta dawo min hankalinta tashe kan maganar, UMUGHLUK ITIBEL babu laifin iyalina a ciki, hasalima baki daya laifin nawa ne, nine na ce dole zamu bi, nine na nuna dole zamu aikata......." Ya ajiiye maganar hawayensa na sake balewa , sai kuma ya dago yana kallonsu ya ce" Na san kana shara'a ne idan kowa na gabanka a zaune ta yadda kowa zai kwaci kansa, haka kuma na san cewa kama fada a tsaye a kuma zaune cewa baka shara'a ka ware na gida, ko ka ware mai arziki, takobinka zata sari du wanni wanda ya kama ta sara, domin ka san zaka mutu , zaka tsay a gabam Ubangiji a matsayin bawa , zaka yi bayanin dukkan abinda ka aikata a duniya koda tsakaninka da tumbinka ne........." "KAI DIN MENENE DIN NADIRAH?" muryar Asadeek a sanyaye ya katse Hanzarin mahaifin NADIRAH Aba Salihu ya dago jajayan idannuwansa masu zubar da hawaye a sanyaye ya ce" Yata ce, ita dayaa tak na malaka a gidan duniya, INDI yarinyata ce" Kai ya sada yana tukar kukan da ta yannayin girgizar jikinsa zaka gane kuka ne yake shekawa abinsa ASADEEK kuwa baya ya koma ya jinginar da bayansa ya lumshe idannuwansa yana tasbihi ga ubangijinsa SHEIK ya kalli sarkin yanka ya masa alamun ya fita Fita ya yi, SHEIK kuwa ya fuskanci Aban NADIRAH a tausashe ya bashi umarnin dawowa ya zauna a waje mai kyau Da kyar da wala haula ya yarda ya hau kafet din, ama firr ya ki hawa kujera wai ASADEEK na waje ba zai hau sama ba Sheik ya yi murmushi yana kallonsa a tausashe ya ce" Bawan Allah, ka dubi girman Allah, ka yi kokari ka shinfida shinfida mai kyau a tafiyarka ta hanyar sanar mana abinda ka sani a kan auren nan da ya juya rana tsaka, kamar yadda ka sani a duniya idan bawa yanada hankali ba tsoron kowa zai ji ba sai na Allah, Akoy ranar fitar rai, akoy kwonciyar kabari, akoy tsayuwa a gabam ubangiji, ka yi kokari kaa tuna su sai ka zabi abu guda a ciki, tsoron dan Adam a duniya, ko na ubangijinka" Ajiyar zuciya ya sauke bayan ya girgiza kansa, a nutse ya shiga magana kamar haka" Umarni aka bamu, cewa zamu bayar da yarmu a matsayin gimbiya BAHIJA, aka kilacemu aka shiga shiryata dan kasancewa mata a wajen UMUGHLUK ITIBEL," Sheikh ya kalli ASADEEK, yana nan a yadda yake, kansa na kallon sama, sajensa da bakin gemunsa lufluf a Kwonce, yannayin da hannayensa suke zai nuna maka a wanu hali yake mai girman gaske Sheikh ya sake sauke ajiyar zuciya ya ce" Ama, ko ka sam dalilinsu na aikata haka?" Sosai yake jin girma da nauyin dalilin da suka sani, ama ya zala wajibi ya sanar koda hakan na nufin mutuwarsa ne A sanyaye ya ce" An hada haka ne dan a kawar da UMUGHLUK ITIBEL daga doron kasa" A zabure Sheikh ya sake fuskantarsa, muryarsa har tana hadewa ya ce" Kar ka yi furuci dan ka fitar da kanka , ka san girman laifin da ka ambata kuwa?" "Na yarda cewa duniya ba matabata bace, na san da cewa idan na guji mutuwa a yanzu zata riskeni wata rana, na kuma san da cewa aikin alkhairina kadai zai sama min sasauci, da ace na yi gudun mutuwar da na gudo da iyalina mun kawo maganar, sai dai sannin da na yi kai tsaye ba zan taba yarda na tunkaroku da wannan maganar a min kallon mai hankali, da kuma sannin da na yi ina iya rufta kaina a ciki , sannan idan sun ci galaba a kaina sunna iya neman wani da aikin ya saka ni amsa, na saka rayuwar yata a hadari, ta matata da ta yar uwarta baki daya a hadari tare da yarda cewa Allah zai karemu, shi zai bamu mafita, shi zai nuna min rana irin ta yau" Aba Salihu ya fada yana sake duban ASADEEK Kan ASADEEK wani irin zafi yake fitarwa hakama kirjinsa har sama sama yake yi na tashin hankali, A hargitse ya dubi bangaren da Sheikh yake har yana hade harshe wajen fadin" UMMA, UMMA ce ta yi jagoranci a lamarin dauko amarya, shin bata san wa aka bata ba? Bata san tsare tsarensu ba?" Gaban SHEIK sai da ya yanke ya fadi, da sauri ya kalli ABA SALIHU gabansa na faduwa ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣2️⃣ Gaban Sheik sai da ya yanke ya fadi, da sauri ya kalli Aba SALIHU gabansa na sake faduwa, sai kuma ya kalli ASADEEK muryarsa a tausashe ya ce" Me zai hanna mu dakatar da binciken haka? Ka fa san zurfafa bincike kai tsaye bashi da dadi fa, kuka bayan wannan ka gaji sosai dan Allah mu je ka huta" Murmushi mai daci ASADEEK ya yi yana kallon SHEIK, muryarsa a tausashe ya ce" Kana tunanin a irin yadda nake cakule da al'uma akoy abinda zai sameni daga dan Adam ya summar da ni?, Ina iya jiran komai daga dan Adam, kaine ilimina, nine alkalinsu, babu irin kwababiyar rayuwar da ba'a kawo min, ka daina yi kamar zaka yi kuka fan kawai na ambaci abinda kake son na gani shekara da shekaru, ka sani tunda na ji ba ita aka aura min ba nake bibiyar UMMA!, Tabas a da ina kin hakan dan na ga irin tsakaninta da Auta, kar ka manta UMMA ma'aikaciyar ANNA ce, watau amintaciyarta ta dogon zamani, ka fi kowa sannin amintacen bawa kan iya zama makashin sarki,nawa aka yi, tun kafin a haifeni ake yi, babu abinda kudi baya haifarwa da mulki, ka barshi ya sanar min matar da kuka zo tare shin ya ga wani abu da ta sani a cikin lamarin ko an rufeta a baibai ne?, Ka barshi ya rufa min asiri ya sanar min wanene AMINU?, Wadinnan abubuwan sunne suka kawo ni garin nan idan na ji su a yanzu a yanzu zan juya kasata, idan ban ji su ba kuwa ba zan koma ba!, Ba dan ina tsoron kar a cin min ba, ko daya, hasalima ji na yi ko menene ai bai isa ya riskeni in ba Allah ya hukunta min ba!, Magauta kuwa a cikinsu muke zagaye, ba wai ni ba harta baran gidana!, .......DAN ALLAH ka sanar min ita matar nan mai dan haske gajeriya mai dan jikin kiba kadan wace suka zo tare ta san wani abu a cikin lamarin?" ASADEEK ya karashe yana kallon ABA SALIHU, wanda shima tunda ASADEEK din ya fara magana ya fahimci tabas matar a kusa fa shi take sosai, kuma ya ji sunnan AMINU dainda cikinsa ya so rikicewa, kai jama'a wannan Aminu dai yana wahalar da shi ainun A sanyayensa ya ce" Allah ya taimakeka, in dai matar da suka zo tare ce kake nufi, wace tamkar itace ja gaban komai a lamarin, ita ta yi tuwo ta yi miya a tafiyar, domin a nanma zuwan sarki biyu wajenta sunna tsare tsarensu, ranar da za'a tafi da NADIRAR ma da kyar matar ta yarda mahaifiyar Nadirar ta ganta, wai kar ta lalata masu shiri a yadda ta sanar min" Hannaye biyu SHEIK ya saka a gaban goshinsa ya dafe goshin nasa, dan irin dukan da kirjinsa ke yi masa ba na wasa bane, gaba daya bai so ace ASADEEK ya ji irin maganar nan haka ba, ya so ace a hankali ya fahimta da kansa ba wai ya ji daga bakin wani ba ASADEEK kuwa jajayen idannuwansa ya daga sama yana kallon oankar dake gudu da dukkan karfinta tana busar masu da zufar jikinsu, ama sai yake ji kamar wace take tsatsafo masu da zufa ne, dan a wajen babu wanda baya alamu na zafi yake ji Idannuwan nasa ya mayar kan Aba yana mai jimke hannunsa, a hankali ya ce " Kana nufin, tana cikin shirin da suke yi?" "ASADEEK" SHEIK ya fada bayan ya dago kansa ASADEEK ya dubi SHEIK, ya sake kallon Aba Kai ya girgiza yana neman soke kansa kasa ya ce" Ba zaka barni na gama jin abinda nake son ji a nutse ba? Ka barni na ji mana ko zan iya musalta abinda nake tunani a kanta, kar ka manta da sunnan da muke kiranta, kar ka manta kanwata a hannunta take, kar ka manta nakan ce da kai ban san dalilin da yasa idan ta zo waje kanwata ke nutsuwa ta daina magana ba, nakan ce da kai ita kadai ce maganin kanwata idan ta rikice da maganar sai ta koma gidan mijinta ita kadai ke rarashinta ta bar maganar sai ta warke, kar manta bata da shamaki da bangarena a kowani irin lokaci, kar kuma ka manta tana da damar da HUZNAH bata da ita a fadata!, Ni a uwa na dauketa shi yasa nake kiranta UMMA, shi yasa nake zama a ci abinci da ita da iyalina!" Ya karashe da wani irin yannayi mai dukan zuciya Aban NADIRAH gaba daya sai ya ji shima nashi hankalin ya tashi a irin furucin UMUGHLUK ITIBEL Kennan wannan matar har haka take da kusanci da shi?, Lalle da ace zai bude masa dukkan abinda ya sani a kanta tabas zai ji masa mugun ciwo haka kuma idan har ya ci gaba da ganninsa zai ringa kallonsa matsayin wanda ya kawo masa mugun labarin nan, masoyi masoyi ne a zuciya fa A sanyaye ya sada kansa ya ce" Allah ya huci zuciyarka, bakin abinda na sani kennan" Da mamaki UMUGHLUK ya tsareshi da ido, kwarai ya fahimci ba gaskiya ya fada ba, ama kuma sai ya gaza fitar da hanyar da zai saka shi karfi da yaji yin biyaya, hasalima ji ya yi zai iya kyale shi ya zabi abinda yake so, fada masa ko kin fadi ya isa da hakan! Ajiyar zuciya ya sauke yana hararan SHEIK wanda ya sake soke kai yana sauke ajiyar zuciya da bawan Allahn nan ya gane abinda yake nufi, gaba daya baya so tashi daya ASADEEK ya san irin haka, lalle jarumi ne shi, ama babu wanda déception irin haka ba zata yiwa ila ba, bai san girman ilar da zata iya yi masa ba, ama ya san tabas sai ta yi masa ila, tunda har aka saka shi a hanya to zai idasa gannin abinda shi kadai ne baya gannin, watau halayar matar nan da yake kira UMMA! Sun jima a haka, sai da ya idasa daidaita dukkan hargitsin zuciyarsa sannan ya sake bude bakinsa, wannan karron muryarsa a wani irin jigace take yana kallon kasa ba ainahin inda ABA SALIHU yake ba , a sanyaye ya ce" Tauyeta kuka yi ko?, Ko ta yarda ta kawar da ni din ne?, Yaya aka yi ta yarda da maganar aurena bayan tana da fada?" Ido hudu SHEIK da ABA SALIHU suka yi, sai kuma suka kalle shi Gannin dubansa a kasa ya nuna wata alama da girmamawa da jun kunya irin ta sarakunta A hankali Aba SALIHU ya kai dubansa kasa shima, muryarsa da datako da girmamawa ya ce" Ka gafarci shiriritar yar HINDU, kwarai bata jin magana, da sakalci a tatare da ita, sai dai tanada amana sosai, tabas Biyaya ta yi mana a kan maganar auren, ta yarda ne da sharadin idan komai ya bayana zata samu salama ta dawo gida" Idannuwansa da suke da ja ya dago a hankali ya kalli Fuskar Aba, shima Aban a lokacin shi yake kallo, hakan ya saka shi fadin" Ta dawo ta samu AMINU?, Aba wanene AMINU?" Aba Kam magangannun sun yi masa nauyi ainun, sai dai du urin kauce kaucensa UMUGHLUK bin tambayiyinsa yake yi daya bayan daya, ko ya kaucewa wata amsar a dole zai bayar da wata, Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" Shi aminun irin soyayar kauye ne suka yi, shi tuzurun kauye, ita tuzuruwar kauye, tunda a kauye dai mai shekarunsu ya jima bai yi aure ba gaskiya, innarda ta nuna bata so ba zata yarda ba, ita kuma tace zata yi jira har innar tasa ta amince, shirme ne irin na yara, domin sunna tahowa innarsa ta kai kudin yan kata biyu dan badangarci ta masa daki biyu a gidanta ta aura masa, guduwoma ya yi nan din wai na je a raba auren baya sonsu, da kyar da fama muka mayar da shi gudu irin na barewa, sai gashi ko kwana uku ba'a yi ba da kansa ya tardoni yana sheda min an samu karuwa matan nasa na dauke da junna biyu , shin har yanzu babu labarin INDI?, Shine na sheda masa na fa yi mata aure, da fushi dai ya bar wajen nawa" ASADEEK harda su talabe haba, kai jama'a yanzu Fisabililahi gasa masan da take ashe saurayin ya dane mata har biyu ita tana cen tana cewa kar ya karki abinda yake nasa ba nasa bane?, Um yarinta kennan, kanwar hauka A hankali ya furta" Allah shi kyauta " Sheikh da yake kunshe dariyar wai Tuzurun kauye da tuzuruwar kauye ya amsa da amen ya Allah Agogon hannunsa ya duba, sai kuma ya mike tsaye a nutse ya ce" Aba" Aba da kansa ke kasa bai dago ba, dan bai taba tunanin jin sunna irin wannan daga bakin UMUGHLUK ITIBEL a gareshi ba, sai da SHEIK cikin murmushi ya sanar masa da shi yake sannan ya dago kansa yana kallonsa da mamaki da kuma girmamawa ASADEEK ya yi dan murmushi ya ce " Ina fata zaka iya yin rigima ?, Ina nufin fada haka" Kallons kawai suke yi su biyun dan babu wanda ya fahimci inda ya dosa Sai fa ya yi wani murmushin ya zauna yana gannin lokacin sallar Magariba ya gabato sosai ya ce" Ina so ne na aikata aiki mai dalili, ba wanda zan bar baya da kura ba, domin a yau ba sai gobe ba zan tafi da ku" Aba kam bashi da abin cewa sai bin dukkan umarnin da aka tsara masa Hankalinsa du ba a jikinsa ba ya mike ya fice ya koma da sauri, suma du suka mike suka nufi bayi dan daura alwallah da kuma kimtsawa komawa Bayan an fito daga masalaci a gaban jama'ar anguwa Aba Salihu yana dan sauri ya zo ya bankade mutumen dake gabansa yana amsa call, mutun mai jikin girma sosai domin katon jiki ne da shi irin na karfe din nan , ga tsayi ga kuma baki Da rashin damuwa ya ce" Haba malan ka kauce a hanyata mana ka wani tsare hanya da waya a kunnenka" Kwarai abin ya ba yan anguwar mamaki, domin babu wanda ya taba jin muryar Aba sama sama haka, hakane ya sa aka dan kalle su da bakuwar fuskar nan, dan shi wannan din gaskiya babuma wanda ya wani sanshi a nan, yannayinsama ya badu mamaki da suka ga ya shiga masalaci an yi sallah da shi Da mamaki mutumen ya nuna kansa ya ce" Kai, kana da hankali kuwa?, Yaya zaka bigeni ina tsaye ka kuma kasa bani hakuri? Hanyar taka ce? Ka iya bakinka ko a wajen nan sai na yi raga raga da kai ba ruwana da furfurar gaban goshinka!" Aba SALIHU ya sake juyowa yana kallonsa, sai kuma ya kalli dan gidan liman, baban magidanci ya ce" Malan Rabi'u ka ga aiki irin na banzayen samarin zamanin nan ko?, Dan Allah hanyar nan ta tsayuwa ce a gaje waje? Bismillah idan tunaninka ni banza ne ka farka domin nan da kake ganina nine sarkin dawakan mai garin nan!, Ka kuwa san ko ba a ba banzaye rikon wannan sai rikakun mutane!" Wufffff mutumen nan ya karaso a kiftawa da bismillah ya shaki wuyan Aba ta hanyar hadawa da jalabiyarsa ya nemi cira shi sama a haka A rikice datawa da damarin anguwa suka shiga kiciniyar rabawa ciki kuwa harda masu gadin gidan su biyu rai bace ala samu da kyar aka raba tsakani kowane na haki aka ririke mutumen nan dake karra cika kumatunsa da iska na bacin rai Da karfi ya warce hannunsa guda ya nuno Aba a gaban jama'ar nan ya ce" Ka ci nasara tunda har ka ja a wajen da za'a lwaceka!, Ama ka sani da wanda baya yafiya ka ja rigimar!, Ina ruwana da wata sarautarka ? Banzar sarautama irin ta garinku!, Ka sani ka yi da mahaukaci domin ba kai kadai ba harta iyalanka idan kana da su sai na ga bayansu! Sai na karar da ku !" Da karfi ya warce hannayensa ya juya ya ringa tafiya irin an bata masa ran nan Nan f aka taru a kan ABA ana ta jajantawa da kuma yi masa Adu'ar tsari, bama kamar Liman da ya ringa mamakin furucin gannin bayan nan, sosai suka yi masa addu'a da raka shi har kofar gidansa sannan kowa ya yi tafiyarsa A nan kofar gidan suka dora zamansu yadda suka saba, kowane sai fadi yake yi lalle saurayin nan wani dan ta'adda ne, ama ba komai ya zo din zai tardo maza zai saka kansa a uku ne, irin kurin nan na bayan ido har lokacin sallar isha'i ta yi suka je suka gabatar suka dawo suka amso abinci a ciki suka zauna sunna ci sunna dan taba hira, shi dai Aba SALIHU hankalinsa du a rabe yake , har dare ya tsala kusan karfe biyu ta yi sawaye suka dauke sai su uku a kofar gida Mikewa ya yi yana masu salama sakamakon alamun da ya gani an masa ya juya ya shige gidan, summa sunna yi masa da fadin sai da safe su kam ba zasu kwonta yanzu ba A nan a zaunen bayan shigarsa mutumen nan ya bayana a gabansu da bakaken kaya sidik Kafin suke yin wani yinkuri ya riko su da hannayensa daidaya ya masu mugun rikon da ya saka su neman agaji ta nufin fara kurma ihu, sai dai basu samu damar yin hakan ba aka shaka masu wata hodar da ta bugar da su gaba daya daga duniyar mutane Nan suka yasar da su suka shige ciki Hankali kwonce ya fito da FATIME dake ta aukin tambayoyi shi kuma yana bata amsa a gagauce yana janta kiiuuuiuu dan sai tirjewa take yi gaba daya ta kasa fahimtar yarensa a bayane Sai da suka fita sannan su suka shige, BAHIJA dake kwonce tana barci daidaya suka shakawa cikin barcinta ya daukota ya yarda ita a nan kan kofar shigar , sannan suka kwashi abubuwan anfaninta dukiya ne da su wayoyinta kaf masu dauke da numbobin UMUGHLUK ITIBEL, komai da komai, sannan suka je dakin su FATIME din suka barbaza nata suturun suka yayaga wasu da mumunar yaga suka zubar a kasss , na mijintama suka ringa yayafa jinnin kazar da suka yanka kadan kadan , suka fito sunna tafiya mai jan kafa sunna didiga jinnin a hanyar har suka fito sannan suka karasa daf da motar dake jiransu suka mika buhun kayayakin sannan suka tafi da sauri a kaffafuwansu wajen da Sarkin yanka ya ajiye nasa dokin dan ya kunce shi su dauki hanya domin SHEIK ne zai tuka motar su kuma su hau dokin, iyayen NADIRAH kuwa su shige bayan A rikice SHEIK ya sake kallon ASADEEK ya ce " Ka fa san akoy Nisa tsakanin Tanut da AGADAZ, ka bani dama na daga mana kar a kama mu!" ASADEEK da ya rufa rawaninsa a saman kansa ya dan kalli SHEIK, tsakani da Allah SHEIK a tsorace yake , zagayawarsama uku a tsayuwar nan A hankali ya juyo wajen da Fatime ke ta dhashekar kuka , kallo daya ya yi mata ya mayar da dubansa gaban motar a tsanake ya ce" Mu je" Motar na fara tafia FATIME ta dago hankalinta a tashe ta kalli mijinta , muryarta a raunane ta ce" Idan fa suka gane mu muka fito da kanmu suka nemi halaka Indin Hindu? Idan fa suka fahimci cewar mun.............mmmmm............." "Inna" ASADEEK ya fada a tausashe ainun FATIME ta yi dif da kukan ta sada kanta muryarta a raunane ta ce" Allah ya huci zuciyarka, Allah ya karra maka lafiya" Dan murmushi ya yi yana kallon hanya Da kamar minti biyu ya dan sake bude bakinsa ya ce" Bana tunanin dan Adam zai kuma samun wannan damar, sai dai kuma idan mutuwa ta riskeni..... ALLAH YA SANYAYAR DA ZUCIYARKI" daga haka ya kame bakinsa , hasalima carbin SHEIK yake ja bayan ya lunshe idannuwansa, SHEIK kuwa tuki yake yi dan gaske, duda rashin kyan hanya a haka yake sarafa motar yadda ya dace , ta yqdda du inda suka tardo jami'an tsaro za'a dage masu su wuce ne dan an san sun zo ana kuma sane da a yau zai dawo domin SARKIN YANKA ya fada Direct gidan.......... 😍😍😍😍😍 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣3️⃣ Direct gidan SHEIK suka nufa , a nan SHEIK ya jagoranci wajen da zasu zauna, waje mai tsari da tsaro Ba su su bar gidan SHEIK ba sai da karfe hudu da rabi ta yi, ASADEEK na tsaye da rawaninsa yana gannin yadda aka basu masauki mai kyau, matar SHEIK wace ke turaka a daren tana tsaye a kan kaffafuwanta dudaa bata san ainahin da wa ake tafe ba tunda ta ga Mijinta ya fitar da ita a irin daren nan ta bada dukkan kulawar da ta dace ta hanyar saukar bakin da mahinmanci Sunna komawa fada masalaci suka yada zango , sai da duka yi sallar asubahi sannan suka yiwa junna salama kowane ya koma gidansa dan hutawa, domin tafiyar ta ja masu dogon zangon da basu zata ba, ba laifi kowa ya gaji danma jiki ya saba da wasu wahalhalun ai da ba za'a iya jurewa ba Cikin nutsuwa ya haye saman gadonsa yana mai Adu'ar neman tsari sannan ya shiga neman barci ido rufe, ama abin ya gagara Yinwa yake ji a cikinsa, ama ya san ba zai iya ci a yanzu ba, uwa uba damuwar da yake kaucewa tana ta so ta yi tasiri sosai a zuciyarsa har ta hanna masa yin barci Du irin yadda yake yin karfin halin kautar da tunanin UMMA ta san tsare tsaren bafansa shin tana tare da su dan kaunar lamarin ko fin karfinta aka yi ta amince ya kasa fita daga zuciyarsa Kwarai ya san baban burinsa ya tarbeta ya tambayeta, sai dai banzan tunani irin nasa ya hannashi hakan, ya fi ganewa bin sawayenta dan ya gani da idannuwansa domun baya tunanin a irin wasi wasin da zuciyarsa ke ciki in har zai iya yarda da kalaman bakinta, ba dan ya taba kamata da wani hali irin karya ba, sam, dan kawai zargi ya rigaya ya darsu a zuciyarsa dangane da ita lokaci daya, zargi mai girman gaske Haka ya ringa cenza wajen kwonciyar ko zai ji dadin yannayin kwonciyar, ama abu ya gagara tamkar yaron dake laluben mahaifiyarsa haka ya dawo yi a saman bed din , ya kula wannan ya kunce wannan har kuraye kirayen wayar tafi da gidanka dake garkame ta fara damunsa ainun Da mamakin gannin kiran masu gadinsa ya daga yana karama a kunnensa, dan ya san dai ya sheda masu barci zai yi in ba dalili mai karfi ba kar a tashe shi, sai ga kiransu ba kakautawa Jin bayaninsu ya saka shi bada umarnin a barsu su shigo, lokaci daya kuma ya zauna yana dan dafe gabak goshinsa, sai kuma ya mike ya shige bayi dan yin wanka, ko ba komai zai so ace da dan karfi a jikinsa ta yadda zai iya fuskantar matan dake cikin rayuwarsa a irin wannan lokacin Ya dan dauki lokaci a ciki sannan ya fito da alkyaba a jikinsa mai ruwan maroon da golding, kansa caje ba hirami a jiki, daga kasan alkyanar kuwa jalabiya ce fara sol da wandonta dogo , sai lulumshe luhu luhu din idannuwansa da suke da bukatar yin barci yake yi ama abin ya gagara Tunda ya sauko sau daya tak suka yi ido hudu, a hankali ta sinne kanta ta lalubo hannun Auta ta jimke dan har ga Allah sai ta ji tsoron kallon idannuwansa jama'a kamar idan yana ganiyar cin zalin dinta wannan lumshe lumshe kamar kwarto?☹️ Gaishe da shi suke yi, kusan a tare, gaisuwa irin wace kowace ke yi masa, kowace da kalar tata , shi kuma yana amsawa hadi da dan sakin dan murmushi har ya dawo kan UMMA dake ta huci itama ta gaishe shi a yannayin da idan tana cikin bacin rai sannan wajen ya dan dauki shiru Umma ce ta ja numfashi tana kallonsa ta ce" Yarona, abinda ake neman yi min a gidan nan yana neman kaini bango ta yadda ba zan dauka ba, sosai hakurina na son zuwa karshe a gidan nan gaskiya, haba dan Allah, da girmana da darajata? Ina kawar da kai ama sai an nunan iyakata?" Nanauyun idannuwansa ya dago ya sauke dubansa a kanta, gaba daya sai ya ji irin tashin hankalin da a da yake ji idan wani ya dan bata mata yau ko diz baya ji, hasalima sai yake sin ƙaryata abinda ke saman fuskarta A nutse ya cire dubansa yana dorawa kan HUZNAH wace itama tata fuskar har wani irin kumkum take yi, ga dukkan alamu itama kalar a kumbure take A dan sanyaye ya ce" Huznah, zan sha tea" HUZNAH ta kalle shi, sai kuma ta kalli NADIRAH wace ta yi tsuru tsuru a dan yannayi na jin haushi ta ce" To uwar iyayin gaure gyare sai ki bani ky na kawowa mijina Tea, hajia mai kwana!" Gaban goshinsa ya dafe da dan mamaki ya kalli HUZNAH, sai kuma ya kalli Umma wace tamkar ruwa ya cinyeta gannin ga maganar da ta yi ama ASADEEK yake maganar yana son tea?, Hala cikinsa ana gaba da ita yai kuma? A nutse ya gyara zamansa ya dubi Umma , a hankali ya ce" Umma, me yale faruwa ne?, Wani abu aka yi ne?" Yar ajiyar zuciya ta sauke, duda yannayin da ya yi maganar kansa bako ne a gareta , ama da sauki tunda ya tambaya, dan haka ta fuskanceshi ta ce"Dangane da matanka ne da kuma Auta, jiya mun zo a tunaninmu kana nan ashe ka yi tafia baka dawo ba, ita wannan ta nuna mana ai ka yi tafia ne, ita kuma wannan ta dubi idona tace itafa ta fadi sako ko ban samu ba? Da na tambayi wani sako fa? Sai ce min ta yi ita gaskiya ta soke cin abincin taren nan idan kwananta ne, wai ta dubi tsabar idannuwana tace min ana iya hannata sirri da mijinta?, Ita kuma wannan din ita dake baba ta biye mata harda cewa ai kwanakin nata zasu kare itama bata son gannin kafar kowa a nata?, Me kennan? Nice na zama tsohuwar banza nake gannin irin haka? Karshe sai na tambayi ita kuma Auta ina take daga shekaran jiya zuwa jiya, budar bakinta tace wai tana bangaren BAHIJA, wai ko tana som zama a cen? Bahijar dake yarinya zata iya kula da ita ne? Ka fa san Auta bata da lafia dole sai ni ke iya mata, ama haka ina ji ina gani suka tafi taren, kennan na yi abinda zan yi ko? Barci ban samu ba dan tunani , ina dakon shigowarka !" Har Umma ta kai aya yana kallonta ne, kallo irin wanda yake son sake karantar harshenta da kuma abinda ke zuciyarta A hankali ya kalli HUZNAH wace itace baba da Auta da kuma NADIRAH, a nutse ya ce" Ke din da girmanki ne kika aikata haka maimakun ki tsawatar? UMMA ce fa?" HUZNAH ta sauke kanta, muryarta na dan rawa ta dago dubanta tana kallonsa ta ce" Allah ya huci zuciyarka shin yaya zan yi ne ni? Ka ga ina zamana sai ta ringa nemana da masifa, na fada mata ni bana so ama a banza, wai tace idan kwananta ne kar ta ga kafar yarinya ko ta tsohuwa a wajen, kennan ni da Umma ko???????" Ido NADIRAH ta zarro, hakama auta, NADIRAH ta gyada kai tana sake kallonsu HUZNAH ta ci gaba da fadin" Sai ta ringa nuna kamar ta fini sannin mijina bayan bata jima da shigiwa gidana ba, ni ban yiwa Umma rashin kunya ba, gani na yi tunda hakane nima a barni da mijina ranakun girkina ko?" NADIRAH ta tabe baki a ranta tana ayana' mijina mijina, da acema ana son mijin naki ne malama sai a yi fadan?' Bakinta dake musmusmus yake kallo har ta zabga harara ta tabe bakin sannan ya gyada kansa a ransa ya ayana' Hum abama yace tuzuruwar kauye' A bayane kuwa ya ce" To ke BAHIJA me yasa kike haka ne?" A dan zabure ta kalle shi jin sunnan da ya kireta da shi kuma yanzu, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya a kasan zuciyarta tana ayana' Kai Alhamdulilah ashe gwara da ban sanarwa innata cewar wani ya fada masa wacece ni, ta yiwu an kawo masa maganar ne ya karyata, uhum ka ji dai da shi!' A bayane kuma Sai da ta tabe baki, wanda ya kula idan ya kireta da Bahija take aikata hakan sannan ta dube shi ta ce " Yo ni me na yi kuma a nan, ni fa ban ce kafar yarinya da ta tsohuwa ba, cewa na yi kafar baba da ta y'a, ina nufin Auta ai itace y'ata ko?" Daga su har Autar kallonta suke yi bayan ta dire maganar ta kuma cuno baki tana gyara zamanta a dole ita ta gama magana kennan, wai Autar ce y'arta yau kuma mai gaba daya, watau ba zata daina cusawa HUZNAH haushi ba ko? Kennan Auta na kiran ASADEEK aba, ita Mama ☹️ Habarsa da ya talabe ya saki yana girgiza kansa ya ce" Uhum, Allah shi kyauta, kin ga Bahija ki kula, bana so ana raina baban mutun, Umma dai da HUZNAH sun girmeki kin ji ko? Ki daina rainasu kin ji?" Irin yadda yake maganar tamkar yana rarasshinta ya saka daga UMMAN har HUZNAR zuba masa ido da mamaki, Auta kuwa dariyarta take ci a zuciyarta, dan dama tunda suka farka NADIRAH ke fadin kar dai ta yi barci ta san Umma tace yau zata kai kararsu ya dace a yi komai sunna nan kar a zaluncesu Auta yake kallo, yannayin shigarta ta yau, irin yadda idannuwanta basa neman rufewar nan kamar yar maye kulun, labewar nan da tsoron nan, uwa uba irin zaman da suka yi ita da Nadirah na kugu da kugu hannunsu rike ya saka shi dubanta da kyau, a hankali ya ce" AUTA?" Fuskarsa ta sauke fararen idannuwanta , a nutse ta amsa shi tana dan sakin murmushi Hannunsa ya miko yana kallonta ya ce" Zo nan " A hankali ta karasa ta zauna a kusa da shi kamar yadda ta saba, a sanyaye tana mai fitar da murmushi ta ce" ABA " Murmushin nata ya saka shi sakin murmushin shima a hankali ya shafa habarta sannan ya kama hannunta na dama yana kallon fuskarta ya ce" Me yasa ga yadda Ummanki ke so, ke kuma kike son daga mata hankali? Ummanki ce fa?, Kin san kaunar dake tsakaninki da ita ya dace ace kina bin umarninta ko?, Kin ga saboda rashin lafiyarki take tsaye take faman ki daina fita ko?" Idannuwanta ta sada, hannayenta na son su dauki rawa kamar yadda suka saba a da, sai dai da karfi yana jin irin yadda take son controling din tsoronta, wanda karara ya gani a cikin kwayar idannuwanta, hakan ya saka shi a tausashen ya kuma cewa" Idan kuma kina da bukatar mutane a gefenki ne ko da dare ki sanar min mana Auta?" Dago idannuwanta da suka cika da kwallah ta yi ta saka a cikin nasa A sanyaye ta ce" ABAHNA, NI BA MAHAUKACIYA BACE" Dum gabansa ya buga yana kallonta, kanta ta sake sadawa sannan ta ce" ABAH ni ba mahaukaciya bace dan Allah Aba, ka barni na ci gaba da zama tare da aunty BAHIJA ko ka mayar da ni gidan SALEEF " "Ba zaki koma gidan SALEEF kina yin abu ana bazaki a duniya ba, Gidan saleef din ba a cen kike koke koken abanki kike son gani ba?, Yaya muna magani ido rufe kina son mayar mana da shi baya? Babu inda zaki je, dakinki zaki ci gaba da zama!" Umma ta fada a kausashe da kuma dan karfi, hakan ya saka Auta jimke hannunsa kanta a kasa , lokaci daya kuma jikinta ya shiga rawa, ya salam, ta zata zata iya din kamar yadda NADIRAH ta sanar mata cewa idan ta jajirce zata iya, sai gashi tana rawa kamar farar takarda a cikin iskar sararin samaniya a gaban UMMAN, to ita ta yaya zata iya cire tsoron matar nan gaba daya a zuciyarta ne? Ta ina zata fara wannan aiki mai girman gaske ne? Aikin nan fa ya girmameta sosai, ta yaya zata fara shi ne? *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣4️⃣ A hankali ya dan sake rike hannunta yana danne zuciyarsa da kokarin ci gana da buga game din UMMA ba tare da ya sdakar da wuri ba ya ce" To menene na kukan a cikin nan kuma Auta ? C'est très simple hein?, Ki cewa mamanki kina sin zama tare da auntynki ba sai ki je ki zauna ba? Duka dai ai cikin gidan guda ne ko? Maganin kuma a ko'ina ana iya baki shi ki sha, wai inama magungunnanki na tabata baki sha na kwana biyun ba, oya tashi ki je ki dauko min maza share hawayen dauko min su dukansu" Kai ta gyada tana dan share hawayen nata sannan ta mike jiki ba karfi ta bi ta hanyar nan ta cikin falonsa Umma ce ta daga kafa da nufin bin bayanta ta ci kaniyarta kamar yadda ta saba, hakan ya saka NADIRAH mikewa tsaye , sai dai idon da ta ga ya zuba mata da alamun da ya yi mata kan ta koma ta zauna ya sakata zaunawa tana jin hankalinta na neman tashi da lamarin, ta sani sarai Auta ta riga ta tsorata da matar nan sai gyaran Allah kawai A hankali ta dago ta dube shi, muryarta ba karfi ta ce" Abahnta, ta yaya yarinya ta nuna maka bata so zaka nemi tirsasata ne?" Idannuwansa dake kanta ya sake zuba mata har yana wani dan kashe girmansu irin ita din dai yake kallo HUZNAH ta kalleta da mamakin karfin halinta da iya shegenta, kai ta girgiza ta ci gaba da jiran nata maganar, dan ta san ba gamawa ya yi da ita ba, ita kam zata je ta ringa fadawa Allah a kan lamarin yarinyar nan, idan tana wani abin har tsoro take bata NADIRAH ta karra dagowa ta dube shi,yanzu fuskarta ta fara hadewa sosai daga yannayin sakewar nan Ido cikin ido ta ce " ina son tarda ita" "Me ya sa?" Ya fada a tausashe yana sake kallon réaction dinta Matarsa ta kalla, sai kuma ta kalle shi, a taysashen itama ta ce" kawai ina son zuwa kusa da ita!" Hanyar ya kalla shima, sai kuma ya yi dan murmushi bai bata damar tashi ba, hasalima a hankali ya ce" zan so na dan ringa samun lokacin da zaku ringa kasancewa tare, gashi kun nuna bakwa son lokacin cin abinci, shin wani lokaci ne zamu ware?" HUZNAH ta sake jingine bayanta a jikin kujerar nan tana jin du abin wani ba wai, kai kishiya? Kishiya ko ta kara ce gaskiya tana da daukan hankali, shekararsu nawa a cikin tsarin nan ba'a taba magana a kansa ba sai ita isashiya ta nuna bai mata ba, da acema mijin nasu na ratsa tantanin halitarsu ne da sai tace dole ai an riga an san dadin abin, to ama babu wannan ita me take yiwa neman fitinar? Shi kuma a zaunen da yake wani irin abu kai kama da kishadi yake ji idan ya kalli fuskar HUZNAH yadda ta cikota, sannan ya kalli ta NADIRAH yadda ita kadai ke harare harare abinta tana kada kafarta ta dama, hankalinta gaba daya ya yi wajen da su UMMA suka shiga Dan murmushi ya yi, watau abinda take yi du da dalili ko? Zai sake yin magana Auta ta fara shigowa, Expression din fuskarta kadai ya kalla ya ji yannayin nishafi nishadin da yake ciki na neman gagararsa, hakan ya saka shi dauke dubansa a kanta yana mai ambaton Allah har ta dawo ta zauna a nesa da NADIRAR da kuma Shi Aban nata, hakan ya saka NADIRAH lumshe nata idannuwan tana dannar zuciyarta da tambayar kanta anya zata iya ci gaba da jure wannan cin zali irin na UMMA? Ummar ce ta shigo itama, fuskarta a washe yanzu, watau ta nanagawa Auta abinda ta ga dama ta huce ko? Ta dawo ta zauna tana sake kallon NADIRAH, irin abinda suka yi da Nadirar jiya zuwa yau tana son ganewa wai a cikin tsare tsaren ne ko menene? Ta ga ai a lokacin baya nan, kuma ta sanar mata baya nan komai tana iya yi a bayan idannuwansa ama sai ta ga sam bata saurareta ba A kausashe ya ce" Ku tashi ku tafi, zan neme ku, banda UMMA" Su ukkun suka mike, sai ya ga kowace na neman daukan hanyarta daban Watau harda AUTA da NADIRAH A cikin sasaukan Furuci ya ce" AUTA, ki bi Maman naki kin ji?" Da Auta da NADIRAH suka juyo sunna kallon fuskarsa, duda sun so fahimtar me yake nufi ama basu yi gagawar yarda da haka din bane, sai da ya masu alamu da idannuwansa sannan ya ga ikon Allah murmushin da ya fadada fuskar NADIRAH, murmushi irin na jin dadi sannan ta kama hannun Auta suka wuce da dan saurinsu Dubansa ya maido Kan UMMA wace harda zarro ido ta yi dan mamaki tana kallonsa Murmushi ya yi a tausashe ya ce" UMANA, ki yi hakuri da su dan Allah, kin san jiya tafiya muka yi cen garin gabas wajen gonakina, ana yin barna a ciki ne kuma ana neman a tayar da fada tsakanin manomana da makiyayan yankin, kin san makiyayi da abin kiwonsa, to fa shine muka je abu karami ya zamo baba domin a dole muka zauna aka yi ta rabiyar rikicin, da na dawo tuni dare ya yi sai muka zauna a masalaci muka gabagar da sallah sannan na shigo, Inaga lamarin AUTA dole zan fitar da ita, abin nata yanzu ya fara kawo yar gardama , duba ki ga ke fa take yiwa musu?, Allah dai ya bata lafiya" ya ajiye a tausashe da siga irin ta lalami, baban burinsa ya kawar mata da dukkan wani shaku a kan fitarsa, da du wani sake sake, ya kuwa kai ga ci ya kamata a cikin game dinta, domin ta yarda da hakan harma ta dora da kalar nata munafurcin na yin galaba a kansa a da ta shiga shashekar kuka da share hawaye ta ce" Idan na ga haka sai na ji hankalina na neman tashi yarona, shin Auta tanada wani wanda ya fi ni ne?, Tana ja baya da ni ne dan ina bata magani ina kuma tursasata cin abinci" Murmushi ya yi yana fan sake dafe gaban goshinsa yana kuma ankare da kiran dake ta shigowa wayar Umman ama ta ki dagawa Umma ta sake dubansa ta ce" Yarona kuma ka ga, dole sai ka yiwa Bahija magana fa, kar ta ringa anfani da damar da Allah ya bata ta kasancewarta yar uwarka ta ringa muzgunawa abokiyar zamanta sannan ni ta ringa rainani " Kai Allah mai mutane, a cikin mutanensa ya halici rikakun munafukan da duka iya tafiyar da rayuwar munafurcinsu cikin kwarewar da ba zaka iya gani kai tsaye ba sai idan Allah ya so ka gannin, da wannan dama da Allah ya bashi ya dake budar bakinsa ba tare da gajiyawa ba ya ce" Hakane, inaga ko harda yarinta dake damun BAHIJA?, Ba laifi in sha Allah zan kwatanta mata, kema sai kin tayani UMMA ni bani da time din abubuwan nan ne ma, ta rikicin cikin gari na ji ko tasu?, Ama maganar cin abincin nan nine nake da wannan ra'ayin, ba dan komai ba dai dan a baki lafiya ki ringa hutawa kema, shekaru karra ja suke yi wannan zama na karfe takwas a dauki wasu lokutan masu wani tsayin yanzu ba naki bane UMMA, sauran magangannun kuwa dole zan zauna da su na sanar masu ke uwa ce a gareni du mai son zaman lafiya ya girmamaki" Magana ne yake yi mata du a dadaure, sai ya fadi wace ya dace ta rikita mata lisafi sai kuma ya fadi wace zata Kwonce tunanin cen nata na cewar ko wani abu na faruwa ne? Fahimtar da ta yi ta fa ishe shi fa yawan maganar ya sakata mikewa ta yi masa salama ta tafi Bayan ta tafi maganin Auta dake hannunsa ya cusa a cikin aljihun jalabiyarsa, sannan ya cire alkyabar gaba daya a hankali ya ci gaba da jan carbinsa yana neman sauki a wajen ubangijinsa har sansanyan barci ya dauke shi a nan saman kujerar, domin kafafuwansa kawai ya hauda sama ya shiga hutawa __________________________________ A ranar UMMA bata kula kiran da aka yi ta yi mata ba, a tunaninta so syke su ji ko an saka masa maganin a abincin, har sai da wata safiyar ta waye, da sanyin safiya ta daga kiran da abin barci a idannuwanta domin ko salllar asubah bata yi ba, yawancin lokutama idan ta tashi ta ga rana ta yi bata yi kwata kwata gaskiya Muryarta a ciki ciki ta ce" Wai dan Allah ku idan kuka so abu kamar Da ya so fita daga cikin uwarsa ne? Haba dan Allah ban saka maganin ba a gaba fa, ama sai wani kirana kuke yi ba dare ba rana ?" "Ke dan Allah ki min shiru da banzan maganarki, ke har kin san yadda da yake yi idan ya so fita daga cikin uwarsa ke da baki taba haihuwa ba sai na kashi?, Ba maganar magani ake son yi maki ba, so muke mu sanar maki abinda ya faru da iyayen yarinyar nan, an neme su an rasa yau safia ta biyu kennan wai sun yi fada da wani mutun, mu muna nan cikin tashin hankalin abin ke kina cen kuna hauka!" Muryar mahaifiyar Bahija a zafafe ta fada har tana huci da takaicin Umma Gaba daya Umma ta rigijo daga saman gadonta lokaci daya kuma jikinta ya dauki mahaulacin bari gab gab gab , haka kuma kafafuwanta suka dauki mijirya A rikice ta ce" wani irin an neme su an rasa, gidan uban wa suka shiga yo? Ina masu tsaron nasu?" "Gidan ubanda kika aikesu!, Fada ya yi da wani mutun mai kama da yan ta'ada, a yadda yan anguwa suka ce mutumen ya masa alkawarin batar da shi da danginsa, maganar da nake maki harta BAHIJA sai da ta wuni a summe bale masu gadinsu, sai da likitoci suka wuni a kansu baki dayansu sannan suka dawo hayacinsu!, Ki gagauta bincikar yarinyar nan dan ni abin nan na kasa amincewa da shi, gashi kina nan kinaa shirme kin ki maida hankali a kan dan aikin da aka baki ba wani ba, ni kam babu abinda zai mayar min da aiki baya na fada maki, wayar uwar ke hannuna sai kira yar uwar tata take yi, ki je ki sanar masu gaskiyar lamari cewa an sace yan uwansu mu babu hannayenmu a ciki, kuma su mayar da hankali su mana aikinmu ko suma da suka rage mu kuma mu salwantar da rayukansu!" Ta sake fada a kausashe Wata ashariya UMMA ta lailayo ta lailaya mata a haulace ta ce" Ke ama mahaukaciya ce !" "Kece mahaukaciyar daba da baki san abinda kike yi ba!" Ta rama itama rai bace, hakan ya saka Umma mikewa tana rarumar tufafi domin zannin kansa watsewa ya yi tsabar firgicewa da kidimewa Zata yi magana Muryar sarkin tanus ta dauke tata muryar, cikin hali naa bacin rai da daguwar hankali ya ce" Salam *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣5️⃣ Cikin hali na bacin rai da daguwar Hankali ya ce" Saurara hakanan mana Laure, kina jina ki san yadda zaki yi da maganar, ni dai ban san ina suke ba, abinda na sani aikina da kike nan kina jan jiki har yanzu ba'a yi ba bayan na tura maki maganin, ke kin san ribarki ce, kamar yada take tawa, shawararki ce ki maida hankali a yi ko kar ki maida na fada maki!" Daga haka ya kashe kiran ya shiga balbale matarsa da masifar da ba laifinta ba, har hutawa yake yi yana dorawa daga inda ya tsaya, fadi yake du itace mai laifi da bata iyawa kanta a komai sai masifafen la'ananen kishi marar anfani, maimakun ta je ta tsaya a inda y'arta take ta karra gargadinta kan haukan nuna kanta kafin a kashe sarki tana nan tana hauka, wai itace harda gayatar wani kato gida bayan an boyeta ne? To ta yi da kyau , ta maida hankali sosai, idan har ta yarda ta yi shirme ta falasa kanta shi ya san inda zai kai kansa ya tsira, tsakaninta da UMUGHLUK ITIBEL kuwa sai ta san ta yadda zata guje masa! Babu abinda ya dada kansa a kas walahi Abubuwa suka taru suka yiwa mahaifiyar Bahija yawa , ra rasa ina zata kama, ta ina zata fara, itama kwana uku kennan yau tana kiran number yar uwarta bata samu, ko a whatsup din ko a kira direct, tun ranar da ta sanar mata dan banzan danta ya saka layinsa na Nijar rabonta da su, Allah dai ya sa ba wata jarabar bace ba kuma, domin idan har ta yi wasan da UMUGHLUK ya damke su sun bani walahi Hijabinta ta saka mai nikaf dan ficewa a boye a taxi dan ta je inda ta boye BAHIJA dake cen kamar mai sabon kamu sai ihu take yi wayoyinta, number balarabenta meye meye, abu dai gayanan ya same su ba shawara ba sasauci ga sarki sai dora mata laifuka yake yi ita daya ____________________________________ Komai take yi jikinta rawa yake har ta gama saka rigar atampar da ta yayumo a cikin suturunta Bata taba tunanin zata ji dan labarin da zai rikitata a kusa kusa ba har ya sakata fita ba alkyaba irin na yau, to dama hakane a duniya mutun marar gaskiya ya fi kowa saurin kidimewa da neman shiga a rikicewa komai kankantar abu Hijabin sallarta daya tak wanda yake warin ruwa da ajiya dan ba wani wankeshi ake yi ba, shi da ba alkyaba ba? Ai bashi da wani anfani tunda ba na sakawa a yagawa mutanen masarautar AGADAZ Idan fa makantar ta nufo zuwa take yi da dukan karfinta Hankalinta tashe direct bangaren NADIRAH Tana zuwa ta samu NADIRAR ita kadai a falo tana zaune, kasancewar karfe tara na safiya ta wuce tana kallon film din hausa a TV tana ta doka murmushi, ta sha shiga irin ta hausawa watau riga da zani na atampa dinki mai kyau mai sauki, dauri ne ta rangada ture ka ga tsiya wanda ya yi wani irin kyau a saman kanta, kanshin da jikinta ke fitarwa kuwa kadai abin takamar kowace mace ne ace tana fitar da shi, sansanyan kanshi mai saka nutsuwa, babu inda baya fitar da kanshin a sasan jikinta har zuwa gashin kanta, akaifunta kuwa har wani daukan ido suke na gyara Ido cikin ido suke kallon junna ita da UMMA Da mamaki take bin UMMAN da kallo har ta zauna saman kujera tana ta wani dan tabe tabe haka a jikinta, ta kalli nan, ta kalli cen Sai da ta gama waige waige irin na munafukai sannan ta dan matso kusa da NADIRAH wace ta kama kanta ta shiga neman hijabinta dan gaba daya bata son wata mu'amula da matar walahi Umma kasa kasa sosai ta ce" Kin ga jiya bamu zauna ba ko NADIRAH?, Du irin yadda na so na salami baki da wuri mu zauna mu sha dariyar diramarki abin ya gagara, gaskiya kin kware ina matukar sara maki, idan kika gama aikin nan ina mai tabatar maki nima sai na maki kyauta taki ta bajinta" Irin kallon da NADIRAH ke yi mata da tana cikin hayacinta da ba zata taba amincewa da shi ba, ta yiwu sanadiyarsa har sai ta kawo kararta wajen ASADEEK, ama da yake yanzu hankalin nata gaba daya ba a jikinta yake ba sai bata gani ba Kullin dake boye a jikinta ta fitar, kasa kasa sosai ta miko mata tana fadin" Shin yaushe ne zaki yi anfani da wannan? Lokaci fa sai ja yake yi NADIRAH" Gaban NADIRAH sai da ya kwonci kwonci ya fadi, ta tsurawa abin ido ta ki tabawa ko da hannunta ne Umma zata sake mika mata AUTA ta fito daga daki dan Inna ta gama mata abinda take yi mata tuni, Innar cema ke ta bige bigen waya bata samu yanzu dai ta ji ta samu mijinta shi yasa ta fito ta bata waje Da sauri UMMA ta mayar da hannunta tana soke Maganin gabanta na faduwa, lokaci daya kuma ta hade girar sama da ta kasa tana jira Auta ta gaisheta ta koreta daga wajen su gama magana da NADIRAH, dan so take yi yanzu yanzu ta bata abin nan idan da hali a yau yau ta zuba masa a abincin kowama ya huta Ba tare da sakewa ba ta gaisar da Umma, daga nesa nesa , sannan zuciyarta cike da mamakin shigar ta UMMA, ashe Umma zata iya zuwa wani waje ba Alkyaba? Ai ita tana iya rantsewa tunda aka yanta Umma da saka alkyaba bata taba ganninta babu ita ba Gefen NADIRAH ta zauna a hankali ta sadda kanta, dan ba zata taba iya sakewa a gaban UMMA ba Kasa kasa sosai NADIRAH ta ce " Dago min kanki!" A hankali ta dan juyo zata kalleta, sai ta sake sinne kan nata gabanta na faduwa NADIRAH ta ja tsakin da ya saka UMMA kallonta, zata yi magana a zafafe salatin INNA Hindu ya katseta "Lah Ha ila Ha illalahu, Muhamadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wa salam, HABU ka yiwa darajar sy gwagwo ka daina ce min ba'a san inda su aunty suke ba, wani irin ba'a san inda suke ba, Habu wannan wani irin magana ne? Shine bake kiranka jiya wuni guda cirrrr ka ki dagan waya?, Habu ina yar uwata da mijinta suke? Wa bilahilazi ana neman a mutu, ana nan a shiga uku! In na yarda Ubana goma!, Kan uba wayo na shiga ukuna!" Ta karashe a haukace, tana idasa fitowa falon gaba dayanta, lokaci daya tana cuje dan kwalin kanta ta yar "Innata lafiya?, Menene?" NADIRAH ta fada muryarta na amayara da alamun tashin hankali Hannaye kawai take ta watsawa, ta yi nan ta yi nan tamkar wace ke hali na maye, gaba daya Nadirah da auta suka kasa tsayar da ita daga yawon , tana yi kumatana rusa kuka tamkar wace aka yiwa mutuwa Da kyar hankalinta ya kawo kan UMMA , wace ta yi tsaye itama hankalinta a matukar tashe tana kallonsu fargaba shinfide a saman fuskarta Hannunta da NADIRAH ke rike da shi ta janye a birkice ba tsoro ko dar ta karasa kusa da Inna idannuwanta tarr cikin nata ta ce" Ina yayata?, Ke ina yar uwata?" Umma ta ringa son nuna mata ba fa su kadai bane ta hanyar fadin" Ban gane hausarki ba fa ni, wace yayarki kike tambayata a nan ni kadai ce mutun?" Inna ta kunce zaninta ta mayar da shi saman cikinta ta daure shi tam, ta fuskanci Umma muryarta a matukar tashe ta ce" baki gane cewar a yanzu na kai matakin da bana tsoron kowa da komai sai mahalicina ba? Ya dace ace kin jima da karantar haka a cikin idannuwana, Habu yace yau dare na biyu kennan da ba'a ga yayata da mijinta ba, wai wata magana kamar ta yan giya ya yi musu da wani mutun ya masa alkawarin karar da danginsa, bari ki ji , gabs daya a tsarin nan da kuka yi babu abinda na yarda da shi, ku kuka sacen yar uwata da mijinta, ku fito min da su ko tarayar tamu ta yi gagawar watsewar da bakwa tunani na rantse maki da Allah a kan haka ko kaina aka sare bani da damuwa dan ban zabi duniyar fiye da kiyamar ba, na san cewa zamani muke ciki mai shudewa tunda uwata da ubana sun mutu nima tawa na kusa mutuwar, ke ina AUNTY FATIME DA MIJINTA!" Wata irin sakaryar juwa ke son dibar NADIRAH a lokacin da ta fahimci inda innarta ta nufa, a hankali ta saka hannunta ta dan matsa kafadar Auta dake tsaye tamkar mutun mutuni tana son fahimtar inda magangannun nan suka nufa Tana zuwa gaban Umma ta kalli Umman, ra kalli INNARTA Inna hindu da bata daina kukan nan ba tana rike ne da hijabin Umma kan sai ta sanar mata ina yayarta da mijinta suke, ita kuma bakinta a dinke, zuciyarta na wata irin rawa da suya tana tunanin ya zama wajibi kennan a kashe auta kafin yayanta tunda mahaukatan nan suka tona asirin nan a gabanta walahi! Muryarta a birkice ta ce" Innata, wai innar birni ce ba'a gani ba? To ama innar birni ai bata da yawoma ko?" " Ba maganar yawo bane, gidan da aka kilaceki aka shiga aka sace su ita da Aban birni bayan an bugar da masu gadi da dayar algungumar!" Inna Hindu ta fada tana fitar da idannuwanta , masifa na ciciyarta dan ta riga ta rike matar nan yau sai ta nuna mata menene hannun surfe wa bilahilazi! "Kilacewa?" Auta ta fitar da furucin a rarabe tana kallonsu Gaba dayansu suka juyo sunna kallonta, sai kuma NADIRAH ta fara dauke dubanta ta sake mayarwa kanm UMMA, muryyarta a matukar sanyaye ta ce" Ama, ina ce mun yi magana mun ajiye, mun samu matsaya daya mun kuma yi biyaya ko?, Inace a kan abinda aka doramu muke bamu sauka ba har zuwa wannan lokacin ko?, Inace tsayin lokacin nan tsakaninmu da ku kune iyayen gidanmu, mune bayinku ko? Inace aikin kwatar rayukanmu muke yi tukuru, ba ji ba gani, innata na tare da ni a nan, ta zubar da gidanta, ta baro mijinta dan burinmu , mu yi mu gama muma mu samu sa'ida, ko kuma akoy lauje cikin nadi ne? Ina nufin ko kuma idan muka gama aikin ba za'a barmu bane muke ciki haikan?" Umma ta kama gefen hijabinta ta ringa ja Inna na ja, a birkice ta ce" Ki cika min hijabi mana na samu damar yin magana!" Inna Hindu da kyar ta sakar mata Hijabin Ama ta yi wata tsayuwa ta kaka gida a gabanta Umma ta yi tsaki ta ce" Kawai daga jin magana sai ki nemi zuba min komai saman kaina bayan nima abinda aka kirayeni aka sanar min kennan har na fito ko alkyaba babu a jikina?, Kun zo kunna ta sakin magangannu a gaban yarinyar nan duda ni ba tsoronta nake ji ba kuma inada damar da zan sakata yin shiru koda a gabanta na aikata aikin nan, ama ku fa?, Zaku zo ku yi tsaye kunna wasu irin abubuwa bayan muma abinda ya daga mana hankali kennan ana cen ana nemansu?" "Ana neman wa? Waye yake neman wa? Da wace siga? Da wani dalili? Ta yaya?, Dan girman Allah ki sanar mana abinda kuke nufi , wani nema zaku yi ne bayan mun san me yake nade a harshenku bayan kyakyawan furuci da shinfidadiyar fuska mai fara'a?" NADIRAH ta sake fada, a wani irin sanyaye, wara irin juwa na dibanta, tana ta son rike abu ama babu abinda zata iya rikewa karshe sai da ta samu kanta a kasa warwas domin Juwar nan sai da tamakata a kasssss A rikice su biyu suka yi kanta, watau Auta da Inna Hindu Taimaka mata suka yi suka jinginar da ita da kujera Auta hankalinta na sake tashi Umma ce ta ci gaba da magana, babu abinda ya dameta da faduwar ta NADIRAH , itama damuwarta ta isheta ana neman dora masu laifin sace mutanen da basu sace ba, a sanninta dau basu sace din ba, in dai ba sarauniyar Tanus ta saka aka sace din ba to fa bata da takamaimiyar amsa , da son convincng dinsu ta ce" Cewa ta yi an fito daga masalaci suka yi fada shi da wani mutun a gaban kowa mutumen ya ce sai ya kashe shi da danginsa baki daya, kuma ga sheda nan an kwashe su, an ce mutumen kamar wani kasurgumin dan ta'ada, wai yannayin halitarsa mai saka a ji tsoronsa ne , shikenan sai ku ce mu ne? Mu bamu dauke su ba" Zuciyarta dake beating da karfi ta dafe tana lumshe idannuwanta zazafan hawayenta suka shiga gangarowa a saman kumatunta Innalilahi wa inna ilaihi raj'une Dishi dishi take kallon yadda rigima ta kaure tsakanin innarta da UMMA babu mai ba yar uwarsa hakuri, ita kuma auta magangannun dake fitowa daga bakinsu ke neman tsayar da numfashinta, bata san haukan nata ne ya motsa ba ko menene har take tunanin matar da take ji a ranta a yanzu fiye da kowace mace a matsayin yar uwa rabin jiki, da matar da take kira Mamah bayan mahaifiyarta ba ainahin wace take zato bace na neman sakata jin kamar zata shiga a hali na hauka ya saka babu wanda ya ji motsin NADIRAH, basu ankara da ficewarta ba, sai karar rufe kofar da suka ji wace ita dinma dan ta murda Ky din wajenta da ta cire ta mayar da shi ta baya ta rufe suka gane cewar wani zai shigo, ko wani ya fita Cikin Umma daga sama sai da ya dawo kasa, lokaci daya ya shiga bada wani kuka kuuuuuuuuuuuu alamu na gudawa na tatara kanta sannan wata makirar zufa irin ta saman goshin nan tace Bismillah, lokaci daya ta karra jin bata yaba fuskantar fargaba da tashin hankali irin na yau, lokaci daya kuma wajen ya dauki shiru ya zanto kamar babu wata halita a wajen , kowa ya yi tsittt hanyar yake kallo da jiran wanda zai shigo, dan babu wanda ya gane cewar fita aka yi, ba shigowa ake son yi ba Wanzuwar shirun da ya yi yawa ya saka INNA HINDU karasawa ta leka Idannuwanta ta kankance tana hango abinda take gani, watau babu KY din wajen, Hakan ya sakata zarro ido ta juyo tana kallon UMMA da a lokacin take ji a cikin jikinta kamar lokacinta ne ya yi, irin yadda zuciyarta ke dokawa da karfin masifa kamar zata bar gangar jikinta Sai da ta watsa Hannayenta, sannan da bakinta ta ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣6️⃣ Sai da ta watsa Hannayenta sannan da bakinta ta ce" Inna Indi?" Gaba daya sai Umma Ta nemi neman wacece Indi a cikin kwakwaluwarta, dan harga Allah a irin lokacin ba lallene in ta tuna sunnanta na kantama bale wai wani Indi Wajen da take Innar ta kai dubanta, sai kuma ta kai zaune ta saka hannayenta biyu kaf ta rangada tagumi kasa kasa tana fadin" Yau kam ana falatsin uwar kowa a gidan nan, ta yiwu bamu san inda su Auntyn suke ba za'a yi tsirenmu da ranmu, kun saka mu a masifa muna zamanmu a lungunmu, na tabata ba zai saurari maganar kowa ba zai hada jiji da jan kanwa ne ya mana cakuden luguden surfen uwar kishiya, innalilahi wa inna ilaihi rajune Indi zuwa kika yi wajensa ki ce masa me?" "Wace Indi? Ta je ina?" Umma ke fada bakinta har yana hadewa Inna Hindu ta ki bata Amsa, da kanta ta gane wace ake nufi, hakan ya sakata kaiwa kasa tana dora hannayenta bibiyu a saman kanta idannuwanta tamkar zasu fado kasa ta ce"Ban gane ba, me zata je ta yi? Tana ina? Dama mahaukaciya ce ita? Bata san ba'a wasa da wuta ba?" Guguwa ce? Kusar kan INNA TA HABU MAKADI ce ta kunce? Menene ya sauka a kanta mai karfin da bai ji komai ba, ya kwasheta daga inda take ta rarafa ta dauke fuskar UMMA da wani mahaukacin marin da ya saka Auta faduwa ta yi zaman yan bori sannan ta dora hannayenta saman kanta tana neman haukacewa Bata gama tantance hannun surfe ba inna ta rike hijabinta da kyau ta ce" Kwarankwatsa ki ce tak na tataka ki a wajen nan, ke baki san na jima ina dakon fuskarki ba zaki dubi idona ki ce yar Hindu mahaukaciya? Kin kusa gama aikata laifi a duniya in dai kina hadawa da irin wannan dan ni ba zan kyaleki ba kafin ki je mai sama ya tambayeki, banza shashasha abinda kike tunani ta je ta yi in dai Indi ce, sai mu zauna gaba dayanmu mu jirayi sakamako dan na tabata a yau yau din nan ba juma'a ba ba litinin ba zamu je inda ba kofa bale taga a ci ubanmu!, Dilla sai tsamin kwartaye kike yi!" "Wayo Allahna, Mamah wai me yake faruwa wayo na shiga uku me yake faruwa ne?" Hindu ta saki wuyan Umma dake kici kici din kwace kanta Umma ta mike tsaye fuskarta har ta nuna alamu ranta a bace ta ce" Ni kika mara? Ni kika daukewa hannu a fuskata? Zaki gane maganata da taki ba daya take ba a wajen yarona , zaki gane ke din ba kowa bace ba idan na je na same shi na fada masa su waye ku, zaki san shari iyawa ne idan kika samu kanki dumu dumu a cikin laifin da baki san hawansa baki san saukarsa ba, harta laifin kisa a yau sai ya hau wuyanki zaki gani" Inna ta daga murya tana rakata da fadin" Sai me, da kisa da ba kisa ba mun san yau sai an ci ubanmu, ki fitar da kan naki, dama ai mun san hakan na iya faruwa !" Tana bacewa ganninta sai kuma ta dora hannayenta biyu tana fadin" Wayo Allahna, ta yiwu habunma ba zan kuma gani ba, Yar Hindu an yi y'a gatanan dai ba tsari, maimakun ki tsaya a san ta inda za'a hau kya tarda zaki ki kai masa nama? Yanzun ko a wace take ciki? Ta yiwu ya yi gunduwa gunduwa da ita, bale ni yar tsurut da ni kamar sauran maye" Hawaye na balewa a saman kumatunta ta kuma cewa" Mamah ina ta magana kin kyaleni, gaba daya kin min shiru, bayan ina ta jin maganganun da ba dadi daga bakinki da bakin Umma?, Mama me yake faruwa ne? Sai na ji wai kamar wai wai wai......" Wasu hawayen suka kuma balewa a saman kumatunta shap shap shap tana kallon Hindu, wace itama jikinta a mace yake ainun ita din take kallo Hannayenta ta miko mata , hakan ya sa ta rarafa ta karasa inda take zaune ta zauna hadi da dora kanta a saman cinyarta Ajiyar zuciya take saukewa, a sanyaye ta ce" Auta, Dole fa sai kin yi yaki da kuka, da rikicewa, da saurin nuna tsoro, sannan sai kin dage da addu'a, na dan kina yi, na kuma san kina da hakuri, ina so ki ninka ne, in ba haka ba kema shafeki zata yi daga doron kasa kin ji?" Auta ta dago tana kallon Inma, muryarta a raunane ta ce" Mamah, tsoronta nake ji sosai, ama yanzu da kuke nan na rage jin tsoronta walahi, kin ga Mamah na tabata ba zaku bari ta cuta min ba ko?" Hindu ta lumshe idannuwanta zuciyarta na yin rauni A sanyaye ta ce" Mu fa bamu isa mu saka ko mu hanna ba, muma da kika ganmu a nan ta ranmu muke , kin ga an wayi gari babu danginmu, babu mahaifiyar NADIRAH, kuma babu mahaifinta, gashi ta je ta tona mu da kanta, bayan shi din baya ragawa masu laifi irinmu" Irin yadda ta kureta da ido ne ya saka Hindu sauke nata idannuwan, a raunane ta ce" Bari ki ji su waye mu, ta yiwu ke zaki yarda da mu, sannan ki yi mana kyakyawar fahimta ko?" Auta dai gaba daya magangannun bakinta sun shafe sai kallon Inna take yi Inna ta shiga warware mata dukkan abinda ya faru a sanyaye, tun tana fada idannuwanta na kallon kas har ta dago tana kallonta ido cikin ido tana yi mata bayani...........tun daga kuruciyar NADIRAH, har zuwa yanzu............... A bangaren NADIRAH kuwa Gangar jikinta ce ke tafia, hankalinta kuwa ya yi nisan da bata gane komai, watau bata jin kira in ji hausawa Da manya manyan idannuwanta take dube dube a falon, bata ga kowa ba, hakan ya sakata fara taka matatakalar ta nufi baban dakinsa wanda take tunanin samunsa a cen Fitowarsa kennan daga bayi, ya yi wanka ne domin bai jima da gama Gymn ba, gashin kansa a jike yake, kirjinsa a bude ya dakata yana amsa waya a karamar wayarsa na maganar kasuwancin masarautar , watau maganar tanada mahinmanci shi yasa ya dakata yake amsawa Tunda aka murda aka shigo ya saka a ransa HUZNAH ce, domin a sanninsa kai tsayen nan ita bata zuwa, a jiya ba irin kiran da bai mata bama a karshe tace da shi ita kam zata fada masa gaskiya bata son wasan tabe taben jiki, kowa ya kama kansa kawai gaskiya ita fa ba wata mai jimawa a waje bane idan ta zo, haka ta kashe kiran hankali kwonce ta barshi zaune kamar sumame yana al'ajabin duniya da abinda ke cikinta, sai gata yau ta shigo, shigowar kuma kai tsaye shi ta nufo, ko bata lura da bashi da sutura a jikinsa bane ko me? Sai da ta zo daf da shi, kamar zata shige jikinsa, ta kurawa fuskarsa ido da duba irin wanda ake yiwa abinda ake son gane fari ne ko baki, sannan ta ringa dauke duban nata har zuwa wajen kirjinsa, a hankali ta tsayar da dubanta a nan kirjinta na dokawa kamar zai bale ya bar gangar jikinta "Hey?" Ya fada da wata murya dake fita daga cen lungun makogwaronsa, sannan dan dabinon dake makogwaron nasa ya yi dama kadan ya dawo tsakiya tsakiya yana dan motsi a hankali Wayar dake kange a kunnensa ya janye a hankali yana furta" Ina zuwa" ya datse kiran ya yi tsaye yana sake kallonta, gannin kamar bata san ta zo wajen ba ko menene? A hankali ya saka hannunsa ya janyota dan gannin ko zata tirje? Sai gani ya yi gaba dayanta ta fado saman jikinsa har dan kwalinta ya fadi kasa Hankalinsa ya ji yana neman tashi, hakan ya saka shi dagota da sauri yana kallon fuskarta ya dan girgizata ya ce" Lafiya? Menene?" Sai a lokacin ta gama yanke shawarar ba zata iya yin shiru ba, ko wace wace, a kan iyayenta ya kasheta idan yanna so Silalewa kasa ta yi tana watsa zannin dake jikinta, lokaci daya ta kai kwonce ta mike hannaye da kafafuwanta ta saka ihun da ya saka shi sake zuba mata ido yana kallon sarautar Allah Neman yin birgima take yi bakinta na fadin" Wayo Allahna sun sace min innar birni da Aban birni, na shiga uku, na mutu na lalace mahaifiyata da mahaifina ban san inda zan samo su ba, innalilahi wa inna ilaihi rajune iyayena ne ala nema aka rasa" Lebensa na kasa ya danne da dan karfi, ba dan komai ba sai dan ya hanna kansa fashewa da dariyar da ta tuko shi yana kallon cinyoyin da ake masa kwalele, uhum su tuzuruwar kauye manya Da kyar ya iya cijewa ya nuna alamun tashin hankalinsa ya duka yana biye da ita har ya riketa ya dagota yana kallonta ya ce" BAHIJA, meye kike fadi haka? Su bafa je aka sace kome? Wani irin sacewa kamar kwondala?" Fuskarsa ta tsurawa ido, shi kuma a dole ya kawar da nasa duban dan kar ya fashe da daria, sai dai idannuwansa na sauka a kan fari kal din pant dinta da ya bayyana sakamakon birgimar da take yi a kasan Daukewar kukanta ya yi daidai da daukewar son ya kwashe da dariyar da yake yi, a hankali ya dora hannunsa saman cinyar tata cen kusa da pant din nata a hankali ya hadiye wani irin wahallalan numfashi ya ringa matsa hannun nasa da dabara yana ta lumshe jarabar idonsa "Zan sanar maka komai dalla dalla , ka yiwa Allah kafin ka kasheni ka nemo min iyayena ka ji? Kuma ka sani basu da laifin komai, gaba daya laifina ne ni dayan nan da ka gani, komai nice na yi, komai laifina ne, ka rufa min asiri kamar yadda Allah ya rufa maka kar ka sako min iyayena a cikin fadan nan, kai baka san me yake faruwa bane, a zaunen nan da kake baka san komai ba, kana ji ko, ni din nan ba kowa bace face gagarumar yar cin amana, nice nan na zo gidanka a matsayin wace zata kashe ka.................................................... Kai, tsaya mana, cire hannunka a nan yanzu yanzun nan, ana maka maganar Allah kana kawo irin abubuwan nan wayo Innat................................." Ta rike hannunsa da duka nata hannayen, tana girgiza kai Idannuwansa ya dago a raunane yana kallon fuskarta, a haka din da ta rike shin babu abinda ta hanna shi domin ya idasa kai hannun nasa ita kuma sai zarro ido take yi A ransa ya ayyana ' dama kashenin kika yi ke kam' A bayane kuwa kasa kasa sosai ya ce" Wannan dinma ai sunnah ce, mai ladan gaske, bari mu dan bata hakinta sai mu ji option din gaba me yake faruwa......... NADIRAH.......yanzu banaa gane komai, ke fa kika bude.....mmmmmmmmmmmmmmmmmmmmm" A yanzu kam sai ta rasa BAHIJA yace ko NADIRAH, kokowa ta shiga yi da tunaninta dan ta tinano me ya ambata yanzu yanzun nan, jama'a kamar yace da ita NADIRAH fa? Kamar NADIRAH yace fa? 🤔🤔🤔🤔 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣7️⃣ Tabas baya gane komai, domin gaba dayanta ya dauketa ya karasa saman bed da ita Sai da ya rikita mata jiki iya rikitawa, sabon salon da ya dauka ne watau sai da ta nemi fasa ihu dan rikicewa da irin salon nan nasa sannan ya auna mata lamarin nan nasa mai wuyar fasara Ya jima yana abu daya sannan ya samu saukin nasa lamarin, inda mararta ta dauki dumin da take dauka a kwanakin nan ta yi wani iri kamar ya ajiye mata wani dutse a wajen Hannunta dake kai idannuwanta a lumshe ya dauke ya dora nasa a wajen a hankali yana dan shafa wajen, ya kula yanzu in dai zai tabata ko yayane in dai har ya shigeta sai ya ringa damkar mararta A hankali ya ce" Ko dai baki samu nutsuwa bane ?" Jajayen idannuwanta ta dago a raunane ta tsare fuskarsa da ido Nasa idannuwan ya lumshe mata, kasa kasa ya sake cewa" Na saka harshena?" Ds karfi ta rintse idannuwanta tana son juyar da bayanta, ama ya kiya, a dole ra tsaya masa yadda yake so din, sai sake nanikar wuyanta yake yi ciki ciki ya ce" Kin ga, idan na yi kiranki dan Allah ki ringa zowa kin ji? Baki san ba kyau ba? Jiya fa da yau ranarki ne, ke ko irin a sayi zuciyar mijin nan bakya siya? Ki dan tausaya min mana maraya ne ni fa"................ Bakinta dake ta neman fasa ihu ta kwashashabe a hankali ta daka kuka irin na sangarta da shagwaba da kuma ambaton maraicin da ya yi tana kallonsa ta ce" Nima ai ina daf da zama marainiyar, kilama na zama, wayo Allahna innar birni" Fuskarta ya zubawa ido, dan kuwa da ihu ta fadi haka din kuma ta wani dafe kyakyawar fuskarta , watau dai kukan na daf da balewa Dan murmushi ya sauke ya gyara zamansa da kyau kasa kasa ya ce" NADIRAH" Dif ta yi da kukan ta dago ta saka idannuwanta a cikin nasa tana kallonsa da Expression din son karra jin furucinsa Dan murmushi ya yi dan sarai ya gane so take ta ji BAHIJA yace ko NADIRAH, ya rab ya so ya jima yana tsokanarta da haka, sai dai gaba daya ji yake yi bashi da karfin yin haka kwata kwata, yayama zai iya yin haka dogon zango bayan kuka take yi da hawayenta? Bai ce ba zata iya yin kuka ba a rayuwa, ama ba zai so ace shine sanadiyar hakan ba, a tausashe, dan ya tabbatar mata eh ya san me ya fada ya sake maimaita sunnanta idannuwansa a cikin nata Ido ta zarro, gudun zuciyarta ya dadu, da sauri ta nuna kanta da yaren bebanci ta ce" A san ice Indi?" (Ka san nice Indi?) Ita da kanta bata san ta iya yaren bebaye ba sam Murmushi ya yi ya gyada kai, a hankali ya ce" Na san ke ce Indi, na kuma san kece yar gidan INNA HINDU, da BABA HABU, da inar birni fa kuma Aban Birni" Kirjinta ta dafe, sai kuma ta yi saurin zarro ido, da sauri ta silalo kaffafuwanta ta mike haihuwar Innar birni ta nufi bayi da gudu halitun bayanta na auka sittin saba'in, hakan ya saka shi zarro idannuwa ya sake zubawa kofar da ta bude ta bari a bude ido yana sauraron zubar fitsarinta a cikin WC har ta gama yana jiyo zubar ruwa da wankewarta ta gama ta fito yanzunma a kidime jama'a ta kasa tuna a yaya take tsaye a gabansa ta yi tsaye ta rike gugu, ko iskar sanyin AC bai ankarar da ita cewa mikowar ingozoma take ba, hankali kwonce ta masa tsaye da bindigun kirjinta ta shiga bayani tana kai kawo irin na oga a office , ko hamshakin da yake yin bayanin da yake so a fahimta, kuma a haka take so ya fahimta , ta yi ya kai sau uku tana masa zannen da ya jima da sani watau wacece imnar birni, waye aban birni da na kauye sannan ta juyo ta ce" Wata rana ne, muna zaman zamanmu, mun gama yin fada da Aminu fa innarsa , innarsa ta leta rantsuwar ba zata yarda da aurenmu ba, na cewa tawa innar ta yi hakuri zan hakura idan ta sheka lahira ko mun tsufa ne ba komai sai mu yi aurenmu, sai kawai innata ta ce zata zo birni da ni wajen bikin kawarta da ta haihu, nufinta kafin mu koma na huce sai mu yi zamanmu, ashe ashe harda nufinta ta ji kishi kishin din za'a yiwa Aminu suren dole da wata yar gidan ladan dake sonsa, kai dai wannan shine farkon shigarmu tashin hankali mai zaman kansa, domin a zuwanmu birni ashe marabinmu da kauyen LABBA kennan, muna zuwa muka tarar da ........" "Ke, dakata min, idan kika kuma ambaton sunnan wani kato a gabana NADIRAH, zan karra nuna maki nima kato ne, kuma dukkan abinda yake iya baki ina iya baki shi , koma fiye da hakan malama!" Ya fada a kausashen da bata taba ganninsa ya yi ba, bayan ya mike daga saman gadon fuska a hade harda su nuno mata hannu, domin yana cikin binta da kallo ido na masa radadin tashin hankali ta wani katse masa farin ciki da sunnan wani kato, wollah kamar ta wanka masa mari ya ji Ido ta zarro ta juya ta ce" Baka da sutura fa " Goshinsa ya dafe dan takaici , jama'a ita tanada ita ne? Gaba daya so take yo ta caza masa kwakwaluwa bayan ana abun arziki Muryarsa da amon bacin rai ya ce" Juyo min nan ki ji, a hirarki idan kika saki kika ringa sako min maganar wannan shedanin mai bin zuciyar mace gidan miji sai na babala maki du abinda na warto, kuma sai na wuni a kanki a dakin nan yau koda mayar da ke zan yi kamar tsohon zani sai dai a dinke ki kamar kwarya!, Aminun da kike hauka kansa yana cen mata biyu innar tasa ta aura masa har sun dauki ciki ni kina nan kina juyani kamar waina a cikin tanda, ki kuma min maganar Aminu ki gani!" Yana gama fadi ya juya a haka dinsa ya shige bayi, hakan ya sakata sake zarro ido tana kallonsa har ya bacewa ganninta Bakin gadon ta zauna tana mamakin dama ya iya masifa da ihu wa mutane haka?, Dama ya iya fada murya a dage haka? Me ta masa? Ba ko tausayi? Ba zai tsaya ta gama masa maganar dan ya fahimci basu san komai ba? Innalilahi wai harda su cewa Aminu da mata biyu kuma da ciki, yo Aminu ko farcen mace ya kalla bayan nata ne? Hum za'a hadata da Aminu kiri kiri Fitowarsa da tawul da karasowarsa bakin gadon ya zauna saman kujera ta bakin hado murya a hade ya ce" Ci gaba" ya sakata sada kai a ranta tana mamakin manyan gaban jikinsa da ginanen jiki irin nasa Murya a tausashe ta ci gaba da sanar masa abinda ya faru dala dala, har zuwan su UMMA garin, wanda daga zuwansu ne aka saka aka kirawota, da kilaceta da aka yi, da irin gyaran da ake bata, a nan ne ya ringa yi mata tambayoyi a hankali, yannayin amon muryarsa kuwa na amayar da déception, yakan kawar da kansa gefe ya dauki dan lokaci yana fitar da huci sannan ya juyo inda take, ya sale bata damar idasa maganarta Idannuwanta na kallon kirjinsa, wajen da ya fi bata sha'awa a jikinsa bama idan baya da riga, a sanyaye ta ce" Shi kadai ya zo ya daukeni, a gaban INNAR BIRNI, tana kuka tamkar ranta zai fita, a lokacin da zata sakani a motarma ta sake jadada min magana kamar haka NADIRAH, DUK RINTSI, KAR KI ZUBA MAGANIN DA ZA'A BAKI, KO KI FESA ABIN FESAWA, KO DUK WANI LAUNI NA HANYAR KASHE ABAN DATAWA, KAR KI CE BARI KAWAI KI AIWATAR KI DAWO KI SAMU YARON DA AKA RABAKI DA SHI, KI SANI SUNNAN HAKA KISA, A JAHILCIN DA AKE MAKI IKIRARI KUWA BOKO CE BAKI TSAYA KIN YI BA , INDIN HINDU KI RIKE AMANAR BAWAN ALLAH MARAYAN ALLAH KIN JI?" Idannuwansa ya lumshe a sanyaye , yanzunma a sanyaye ya sake zuba idannuwansa a cikin nata yana kallonta Haka kawai ta ji ba zata juri kallon ba, dan bata daba gannin idannuwansa da rauni ba, bata saba kallon idannuwansa na neman agaji ba, bata san haka a tatare da shi ba Da kyar ya iya cijewa, ya sake bude bakinsa a sanyaye ya ce" Dan Allah, kar ki ce min a zuwanki gidan nan, a fahimtarki harda HUZNAH a cikin wannan rikici kin ji? Kin ga HUZNAH matata ce, matata ce wace ta nuna min sarki ko ba sarki ba tana so na, kuma na yarda da hakan Nadirah, nima ina son matatah, dan Allah kar ki ce min harda ita a cikin wa'inda zasu hadani da bugun zuciya?" Haka kawai ta ji wani irin suka a daidai lokacin da ya yi furucinsa, haka kawai ta ji wani irin zafi a cikin kahon zuciyarta, har ta ji kamar wasu hawaye na cika cikin idannuwanta A hankali ta ringa jin sanyin da bata ji a dazu, harma ta samu a sanyaye ta janyo abin rufar dake saman gadon ta dan raba a jikinta Idannuwanta da suke ta yawo a tsakiyar tsadaden dakin ta maido sakan tsadadiyar kafarsa mai dauke da ni'imtatun kashin jiki luflufluf sun yi baki sidik sunna ta sheki, sannan ta ajiye a kan yan yatsun kafarsa masu tsayi summa samansu akoy gashikan nan Kanta ne ya sara mata, lokaci daya ta ji wani irin zufa da zazabi na son keto mata *HUZNAH* sunnan da mamalakin sunnan , halitar da bata taba kayar mata da gaba ko sakata a hali na jin kishi a da ba, me yasa ambatonta a cikin wasu kalamai na bakon rayuwarta a yanzu suka sakata jin sunnan gaba daya bashi da wani tsari ko dadi a baki? To ita me yasa iyayyenta suka saka mata wani wai HUZNAH? Filon cen filon kawai, sam bata da tsari kwata kwata fa sai kyan jaraba! "NADIRAH" ya fada a sanyaye yana so ta yi masa bayani, duda irin faduwar masa da gaba da bayanin nata ke yi na yanzu, dan sam baya so wani abu mai zafi ya fito daga bakinta a kan HUZNAH, anya zai jure na HUZNHA kuwa? Huznah matar rufin asirinsa ce, ya kirta nata ba dadi ta dawo ta likun masa, a ransa yake ji Huznah matar da zata tarbi mashin da aka harbo masa ce ba ta labe a bayansa ba, idan kuwa ya ga akasin haka an shige shi sosai Walahi Ita kuma da ta dago ta zubawa jajayen lebensa ido sai ta ji a nan fa gaskiya kamar sarki bai yi adalci ba, yo ta yaya zai ringa saka H a karshen sunnan HUZNAH yana wani karasa fada a sanyaye ita kuma ya wani ce NADIRA gatsau ba sakayawa? Oh wato shine namiji mai nuna ya fi son daya fite da daya ko? Irin wa'inda basa tsoron tashi da shanyayen jiki ko yayane? Gannin ta kure shin nan ya daka shi lumshe idannuwansa yana ayana' shikenan, kasheni zasu yi, zuciyata ba zata jure ba' Baki ta murguda tana sake rufe jikinta ta ce" Wannan kayanka ce, da ita ko ba ita duka lamarinka ne, ni ban sani ba gaskiya, na UMMARma ni ba komai na sani ba, kamar dai inaga harda kwartanci tana yi!" Tana gama fada ta mike tana jan bargon hadi da neme nemen atamparta a ranta sai mitar abinda bata san dalilinsa take yi ba........................................... *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣8️⃣ "Wani irin kwartanci kuma?" Ya fada yana juyo da ita bayan ya mike Lululu din da take ji ya sakata dan jinginuwa da jikinsa, muryarta cen ciki ta ce" Juwa nake ji ASADEEK, ina so na je kusa da Innata kafin hukuncinka ya same mu " Shiru ne ya wanzu a wajen na dan lokaci, a hankali ya dora hancinsa a saman kanta yana sinsina , muryarsa cen ciki ya ce" Me yake hadasa maki juwa ne? Ko baki da lafiya ne?" A hankali ta dora kanta a saman kirjin nasa tana sake lunshe idannuwanta, kanshin jikinsa daban ne, kanshin jikinsa mai dadin gaske ne, bata taba jin kanshi mai sakata jin nutsuwa irin haka ba, a hankali ta ringa dan matse kaffafuwanta, domin irin abinda zuciyarta ta raya mata daga jin kanshinsa sai da ta ji a ranta kamar ta zama yar iska fa? Muryarta a raunane ta ce" Walahi ban sani ba, ni dai dazu da na tsorata ne na jita sosai, dama ina jinta yan kwanakin nan ama ba wani sosai ba , inaga idan raina ya bace ne nake jinta" Hannunsa dayan ya saka ya rungumeta sosai a kirjinsa, ya karasa saman kujera da ita ya zauna tana saman kirjinsa Idannuwansa ya lumshe tana kwonce a kirjin nasa, bai san dalilin da ya sa yake ji a ransa a kanta yana iya jure komai, har ji yake yi koda da amincewarta ta amshi magani dan t kashe shi zai iya yafe mata, kome yasa? muryrsa a sanyaye sosai ya ce" Kin san UMMA, tamkar mamanmu muka dauketa, bama kamar Auta, idan ani abu ya fito Auta zata fi kowa shiga a halin tashin hankali ko?" Kanta ta dago tana kallon lebensa, tun dazu ranta raya mata yake yi ta kama ta yi ta tsotsa , bata san dalili ba, ita dai ba yar iska ba ama kuma abu irin wannan na mata yawo a tunaninta na kimtsatsiya? Kan nata ta maida da sauri dan kar ta aikatan, a hankali ta ce" Aa, Auta ta fi kowa shiga halin matsi sanadiyar matar da kake kira UMMA, mai sunnan maman Aba ta fi kowa shiga tsanani a tare da ita, sai ko matarka, kaima ka shiga ama ba a jikinka bane ai..............................." "Kina nufin, kin san da abinda ke jikin HUZNAH?, Kina nufin shima aikin Umma ne? Kina nufin itace ta saka bana iya shigar matata?" Matsar da ya yiwa hannayenta, da furucinsa suka karra zaffafa zuciyarta Tana kallon idannuwansa ta ce" Cikani " Sai a lokacin ya kula ya mata matsa mai dan karfin da take iya yi mata rauni A hankali ya sasauta mata , ita kuma ta mike ta karasa ta dauki kayanta ta kabe ta saka abinta ama ta dunkule pant dinta ta dauki dan kwalinta ta kabe ta daura sannan ta juyo ta ce" Babu iyayena a ciki, ko me zai tardoni ya sameni ni kadai , idan da hali dan Allah ka barni na je Tanus dan neman iyayena!" Dagowa ya yi yana mai gardama da tunaninsa cewa yar gidan Hindu ta yiwu tanada aljannu , a saukake ya ce" Babu inda zaki tafi!" Ja ta yi ta tsaya tana rike kugunta ta ce" Kana ji fa aka ce ba'a san inda inna take da aban birni ba?" Baki ya tabe yana sake kallonta ya ce" Eh , kuma nace ki je ki yi zamanki a dakinki, saura idan an jima kar ki dawo turaka ni sai in zo tunda na matsu" Wani haushi ya karra rike mata wuya, haka fa, tunda ita shine aikinta ai dole ya ce haka, ba zata zo din ba a yi gunduwa gunduwa da ita! Sai da ta karasa kusan katon hotonsu shi da HUZNAH ta zubawa hoton ido, haka kawai ta ji hoton ya mata mugun muni a idannuwanta, dan haka sai ta janyo kujera ta taka tsaf ta sauko shi kasa ta kifa shi sannan ta zagaye shi tana zabgawa hoton harara ta fice Idannuwansa a ware yana kallonta har ta fice ta bar wajen ranta a bayane da bacin rai, a fili ya samu kansa da sakin murmushi ya mike ya karasa yana lekenta harta sauka ta nufi corridor din , hakan ya saka shi sakin wani murmushin ya girgiza kansa ya juya ya nufi wajen wayar tafida gidanka ya shiga neman bangaren UMMA A kalla ya yi kira ya kai sau biyar sannan aka daga , aka kuma yi shiru Shima shirun ya yi har sai da ya ji muryar Umma kasa kasa tana tambayar waye? Hakan ya saka shi a kausashe ya ce" Bata wayar" Jiki na bari wace ta daga wayar ta mikawa UMMA wace ta ji kamar zata summa daga tsayen da take Muryarsa ya sakawa alamun tashin hankali ya ce" UMMA, taushe rabonki da Bafana? Ina nufin kun yi waya da su a kwanakin nan?" Cikin UMMA ya yi wani irin murdawa, zufa ta shiga karyo mata, muryarta na rawa ta ce" Wa, wa, wani abu yace na yi ne?" Lebensa ya dan dantse, sai kuma ya saki ya ce" Kamar yaya wani abu Ummana, wani abu ya faru ne ban sani ba? Yanzu Bahija ta zo tana kukan wai ba'a ga Bafa da sarauniya ba, wai an sace su, ni na rasama me zancen nan yake nufi, ama ganinan zan sauko na ji meye hakan kuma? Kafin na zo zan saka sarkin yanka ya fara yin gaba , inaga zan je tanut din yanzu yanzu in sha Allah, dan bana son karamin rikici irin na rebelle din garin nan!" Salama zata ce? Ko karin rikicewa da kidimewa? Ita dai ta ji wani abu mai sunna sasauci a kan dazu na zulumin an kaita gaba shikenan tata ta kare, a yanzu kuwa sai take tunanin tabas sunna iya gujewa hukuncinsa, hakan ya sa ta nuna rikicewarta a bayane harda su fadin bara ta shirya da ita za'a tafi, ba zata iya zama a nan ya tafi shi kadai ba, wani irin sacewa? Sarki guda? Lalle da an tsokalo tsuliyar dodo walahi! Katse kiran ya yi da wayar a hannunsa, sai kuma ya yi murmushi yana girgiza kai kasa ka sa ya ce" Ta yayama zan tashi kai tsaye na sawaka maki hukuncinki? Dole ne ki fuskanci fargaba, tashin hankali na yau daban na gibe daban, dole ki gane ba sai an kasheka kadai bane aka sakaka a uku, babu abinda ya fi tayar da hankali irin fargaba, da rashin sannin abinda ake ciki, in sha Allah zan sace sun summa a yau da taimakonki zan kawo ku na saka ku a halin rayuwa ko mutuwa!, Sai kun fadi su waye ku da bakunnanku! Da ASADEEK kuke magana!" Umma kuwa a rikice ta ringa doka wayoyin sarauniya da shi sarkin da kansa Da kyar ta samu aka daga, hankalinta a cakule take sanar masu abinda ya faru, har kiran da ASADEEK ya yi mata Bafan Tanus da ya ji hankalinsa na neman tashi da lamarin ya ce" Kina nufin, a tunaninsa mune aka sace?" Umma ta tabatar masa da eh Ya sake cewa" Yanzu nufinki zamu fita mu buya har a kashe shin ko me kike nufi?" Umma dake share zufarta ta ce" Haka nake nufi, yanzu haka da shi da ni zamu taho bincikar abinda yake faruwa, zan san yadda na yi aka bani madararsa na zuba maganin nan a ciki, gwara idan ya zama gawa mu san yadda zamu batar da dan balaki!, Bari ka ji ba zan taba yarda ya ritsa da Ni ba, muryarsa kadai abin tashin hankalina ce, bale ya kamani da mugun laifi!, Bana ciki, ina so a yau yau na kashe shi idan ya so ko me zai biyo baya ya biyo! Na rantse sai na zuba masa gubar nan a yau yau, ka shirya hawa kujerar garin AGADAZ, ka shirya yaki da du wani dan buro'uban da zai nuna bai san zancen ba, ka shirya birne gawa biyu a yau domin ina kashe shi zan kashe MARIYATU kanwarsa idan ya so sauran sai na wulakanta rayuwarsu, sai na yi fatafata da rayuwarsu kafin na halaka su, yadda ta sauke tafin hannunta a fuskata sai ta ci kashina da bakinta!, Maza ka shirya ka fita da banzar nan, saura ku yi yadda za'a gane, kubar abin a matsayin saceku aka yi, kowa da kowa ya gane haka kafin mu iso!" ...........Baki dadara fa buga wasan ba kennan?..........uhum wanda baya jin bari sai ya ga uwar bari😂😂😂😂😂😂........ READERS MUN KUSA GAMA SHI FA🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️ *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 5️⃣9️⃣ Idan baka iya kama barawo ba, shine zai kama ka Umma ta yi shiri cike da tabacin za'a yi tafiyar nan da ita bayan kamar awa biyu ta yi fita ta kai sau uku, ama shiru bata samu ganninsa ba, hasalima kofarsa bakin dakaru ne ta gani wa'inda ba zata ce ta taba sanninsu ba, sun nuna mata barci yake yi, a irin lokacin da tuni ya kusa karasawa garin TANUT ba tare da sanninta ba Yan magana sun ce ice da zafinsa ake dukansa a lokacin da yake tunanin yana tare da mutanensa na hannun dama a irin lokacin aka ainahin sace shin daga shi har iyalinsa , watau shi da matarsa da kuma yarsu mace cilo inda aka sheka su a duniyar barci aka yi doguwar tafia da su wace basu gane komai ba aka kai su boyayen ma'adani mai dauke da dakunna masu duhu da tsayi tamkar gidan yari, an wadatasu da dukkan abunda zasu iya bukata kama daga wajen kwonciya katifu biyu, abin rufa, buta , darduma, ruwa, abinci, sai dai ba'a zuba masu kayan shayi ba, shayi irin na bugaje, shayin da buzu na iya shiga halin kaka naka yi idan ya yi wuni daya tal bai sha shi ba, abinda ya fi kayan maye saurin rike zuciyar buzu, domin abu ne da ya rayu da shi tun yana karaminsa, ya zamto masa jinnin jikinsa zai fi gane ya wuni bai ci abinci ba da ya wuni bai sha shayi ba! A cikin dokar dajin suka tsaya , motoci ne irin Mitsubishi manyan nan masu baya bude na shiga sahara, a kalla sun kai su goma sha daya domin a wajen sun hadu ne da manyan ikon kasa wa'inda ya yi kiransu a hanya ya kuma sanar masu ga inda yake so su hadu, domin ko ba komai bafansa SARKI ne, koda garin da yake mulka dan karamin gari ne bstansa bat lokaci daya ba abu ne mai sauki ba bale garinsa ba karamin gari bane fit, dole sai an yi zaman nan dan su ganewa junna Kowane shi yake kallo, inda yake tsaye cikin shiga ta farin yadi kall, ya nada rawani na farin rawani kal, kafarsa sanye da takalmi baki sidik , irin takalmin nan mai yar siririyar igiya , hakan ya sa ake gannin fara kal din kafarsa da kuma wajen tsintsiyar hannunsa, Dinkin simple dinki ne ba gari da yar ciki ba, dinki ne irin sakaken nan ba mai lafewa a jiki ba sam, sai dai duda haka damatsunnansa a rike suke tak a jiki sun kama shi tak kakar zasu tsage Tunda ya tsaya fuskokin wa'inda ke laye yake bi da kallo, irin kallon nan na son karantar kowa abinda yake kan fuskarsa, domin ai labarin zuciya a tambayi fuska Sarkin yanka kuwa a tsate yake a gefensa, tsayuwarsa irin ta a mutun nan, shi kadai sai ka ji ya fitar da huci kamar bijimin sa , idannuwansa kuwa ba zaka so ka yi ido hudu da su ba a irin wannan lokacin A kan fuskar sarkin DOGON DUTSI ya sauke dubansa, sukaiwa junna kallo na kirki sannan ya dan sauke murmushi kadan kafin ya sake fuskantarsu a nutse ya ce" Ba zaku min tambayar dalilin dauko shi da na yi ba? Ko ba wannan ke damunku ba?" Elhaji Idriss ne ya sauke numfashi a nutse ya ce" Allah ya karra maka lafiya UMUGHLUK ITIBEL, dole hankalinmu zai tashi, wannan fadan cikin gida ne ko na waje? Munada hurumi a ciki ko bamu da shi?, Me yasa harda matarsa da yarsa? Kuma a ina ka boye su?" Me suka yi da tsanani har haka?" Da girmamawa, da kuma gannin girman Elhaji Idrisss a tausashe ya ce" Alhamdulilah, tabas wannan rikici ne da ya hade rigima biyu, ta cikin gida da kuma ta waje, kusan shekara hudu kennan da na kama takardun dukiya ta marigayi sarkin Agadaz, dukiya mai tarin yawan da aka nema aka rasa, har aka so yin rigima a kan hakan ama abin ya yi tuwo ya yi miya, aka zauna a haka nima na yi shiru na zuba ido, ba dan ban san adadin dukiyar ba, ba kuma dan ban san a ina da ina suke ba, sai dan na san ko waye yake rike da dukiyar nan zai falasa kansa wata rana, ko ya cita a hankali ko da garaje dukiya ce da bata boyuwa, dole wata rana sai ya falasa kansa da kansa, domin zinari ne na yankin rijiyar wuta ta gabas, wace take ta ainahin jinnin marigayi, ya gada take dauke da takardu har kwaya tara na nan Nijar da manya manyan kasashe masu fitar da Zinariya, wa'inda suka saka hannu cewa rijiyar nan zata zamto gado ne wa Namiji , idan sarki ya samu maza da yawa tasu ce, idan kuwa mata ne kadai da shi zata zamo ta talakawa ne!, A lokacin da aka zo rikicin rijiya da takardunta tun a lokacin da na sanarwa sarki cewa ba zan taba zaunar rijiya ba, ta talakawa ce!, Tatalin arzikin kasata ce, tun daga lokacin abubuwa suka ringa bilowa, karshe bayan rasuwarsa aka nemi takardu harda na gidan azurfa dake cikin kauyen Ingal ba'a samu ba! Daga wannan ranar na yi shiru da bakina, ama kuma na damu mutanena na daji na baza su du inda na san akoy dukiyata da ta talakawana na basu damar dora kiwo, noma da daba, ta yadda sako zai same ni a kan gaba!" Ya dakatar yana duba agogon hannunsa, ya juya wajen da su SHEIK ke tsaye, ya sake juyowa ya dora da fadin" Ya yi kokari sosai, domin ya dauki shekaru bai je ba, bai aika ba, sai dai mun fi shi juriya da hakurin jiranshi, tunda mu a wajenmu muke, kuma Allah ya ara mana aron rai da lafiya , Bai fara turawa ana masa bincike ba sai nan da shekaru hudu da suka shige, a lokacin yake dan bincikensa, har ya yi rashin wayon zuba mahaukatan karya jefi jefi suke rayuwa da mu dan su gane me muke ciki, a ciki akoy wannan wanda shine baban yaronsa na hannun dama, kuma shine wanda ya tsorata ya sake shi da wuri ya kama mu cikin hikima yake masa aiki yana zayane mana komai, duda ya iya takunsa, ba lale ka san cikinsa ba,........na kayade maku, mutuwar sarki ciwon ciki ne wanda kowa ya sanshi da shi, ama mutuwar marigayiya guba ce mai kumbura ciki, ita ta kashe uwata!" Ya idasa a kausashe yana kallon yadda suke zarro ido , wasunsu har sunna jan rawani baya sunna kallonsa Da tarin mamaki Kambori ya ce" UMUGHLUK, kar ka ce da mu Asarki nada wani abu a cikin hakan?, Idan haka ne ka fitar mana da maci amana mu sare kansa da hannayenmu, domin ba zamu taba bari irin haka ya wuce banza ba!" Daga gefensa , sarkin garin Dosso a tsanake ya ce" Bama wannan ba, yaya nake ji an ce da yarsu, a sanina yarsa mace daya ce jal, kuma ba ita bace ka aura kwananan? Ko ka kamata da wani mugun aiki ne?" Ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya ce" ba ita suka aura min ba, wata suka bani a matsayin ita ce" Wannan abu shi ya karra girgiza masu zuciyoyinsu, domin dai babu wanda bai san abinda hakan yake nufi ba, tabas bayan kishirwar arziki , ta mulki ta shiga, idan kuma za'a bi tarihi dama mulkin haye ya yi masa , dan yanzu yana harin babar kujera ba mamaki, babu wanda mulki ya fi wahalarwa kamar wanda ya yi masa shige da karfi ko ya siya, Yawanci sun ajiye maganarsu ne kan ya yi yadda zai yi da shi da du wani mabiyin bayansa, watau koda hukuncin kisa ke kansa, ya aiwatar sunna tare da shi Kwaya biyu ne suka nema masa sasauci, sasauci a baki sai dai baban tashin hankali a zuci, domin sun sani da a kwacewa asarki sarautar nan gwara a kashe shi, sun nema masa sasaucin hukunci ne cewa idan har shi ya kashe sarauniya a kule shi a kaso cikin bayin da ya saka kaso na kulin rai da rai, yarsa kuwa idan bata da wani laifi ana iya sakinta, ita da mahaifiyarta, in kuwa suka tsaka tsandam wuka ta sha jinni kawai Da wannan suka rarabe da tsayuwar jejin, sannan ya sake kadaicewa da SHEIK Sosai Sheik ke karra tausarsa, ya san shirun nan nasa ba yana nufin baya jin ciwo bane, ba kuma yana nufin ya kyale bane, duda ya fara kai duka yana tsoron abinda ya boye a karkashin zuciyarsa Dan ajiyar zuciya ya sauke, a sanyaye ya ce" ban san ta yadda zan binciki HUZNAH ba, ina matukar jin kunyar sanarwa HUZNAH cewa a wajenta kadai nake ba namiji ba, haka kawai nake ji kamar nine ban yi mata adalci ba, sai nake ji kamar ni na yi sake wani abin ya sameta, idan har ta ji dacin hakan yaya zan rarashets?, Idan ta yi kukan hakan me zan ce mata?, Ina matukar jin kunyar amsar da zan iya bata " Da tarin tausayawa Sheik ke rarashinsa, yana karra nuna masa komai na duniya mukadari ne, in sha Allah itama ba zata dauki komai da zafi ba, kasantuwar abu a haka kuma Allah ya hukunta bata da yadda zata yi, fatana Alllah ya sa akoy maganin abin, domin idan babu maganin abin kam matar nan in har wannanma itace gaskiya tana da kin jin tsoron Allah, to ina zata kai hakin mutun ne Fisabililahi? _________________________________ A bangaren NADIRAH kuwa tana karasawa bangarenta ta tarar da Hindu da Auta a zaune rike da carbi sunna ja, hankalinsu a kan kofa kowane kana kallon fuskarsa zaka ga tsantsar tashin hankali a kan fuskar tasa A zabure Hindu ta mike tana kallonta, a rarabe ta ce" Yar indi yaya dai? Zo mana kar ki fadi" A sakalce ta karasa ta rungumu a jikin innarta, wace ta silale da ita saman kujera Muryarta a kurya ta ce" Auta taimaka min da ruwa , ama dan Allah matsa min lemun tsami da siga a ciki ko na ji dadin bakina, kuma ki taimaka min da gorin innata a saman gado ko na daina jin tashin zuciya?" Innarta dake rike da ita ido ta zuba mata, irin yadda take ta langwui ya sakata zarro ido, ta kalli Auta, ta kalleta A kausashe ta ce" ke dan ubanki ki sanar min abinda ya faru dala dala komai da komai da kika je cen, indi kin sanar masa su waye mu?" Da sauri ta kalli innarta, sai kuma ta kalli Auta, wace ke tsaye tana kallonta itama Kai ta sada tana murza yan yatsunta, hakan ya saka Hindu idasa kwashewa da salati tana rafka tagumi ta ce" Yaushe aka ce za'a kashe mun?" Auta ta kalleta a tsorace, hakama NADIRAH, NADIRAH ta ce" Kashemu kuma?" Hindu ta nuno mata hannu a watse ta ce" Kashemu mana dan ubanki, haka ai yake hukunci, ke yanzu idonsa idonki kika ce masa mune yan ta'adar da muka zo kashe shi ko?" NADIRAH ta turo baki, sai ga hawaye shap shap shap ta shiga sharewa tana kallon innarta, da hannunta ta ce" Inna, bama wannan ya fi yi mini ciwo ba, wai sai ya ce NADIRA gatsau, ita kuma yace HUZNAH, innata me na masa da zafi? Inace in kina kirana har lumshe ido kike yi, kece kika ce du duniya bakya jin dadin sunna irin nawa ko? Wai wani Matata ko kunya baya ji s matsayinsa na abanku!, To ta Allah ba ta mutun ba, da yace kar na kuma masa maganar Aminu yanzu na fara dan Allah ya kasheni ya huta!, Yo inama dalili wai Fisabililahi ashe ya san wacece ni nake zaune tun sarai yana wani ce min Bahija, bahijar nan sai na ci uwata ni din nan innata Allah kuwa, kuma mu jira shi ya zo ya fadi hukunci na san dai bai fi saki ba, ya sakeni mu karra gaba ba cuta ba cutarwa ah to!" Auta yadda ka san zata kifa haka take kallon salamamen tuburaran bakon iya shege a gaban idannuwanta Bata idasa tantancewa ba ta kifa din a lokacind a Inna da zafin rai ta ce" Cuta ta nawa kuma dan ubanki da cikin ina zamu je? Ai du tsiya mun liku sai dai hakuri kaska a jikin kare?.......... Wayo udona😭🥹🥹🥹🥹 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣0️⃣ A kusan tare muryoyinsu ke tambayar CIKI? idannuwansu a waje Shiru inna ta yi tana kallonsu, bama kaamar y'arta da ta tino irin nata haukan, watau nufi irin na nata cewar zamanta da zaki na dan lokaci ne, hum, koda yake tama kyaleta ne, da kanta zata cenza ra'ayi tunda gashinan karara ta nuna bama kashe bane ya fi bakanta mata irin runanin yana kiran dayar da mene, dayar kuwa da me? NADIRAH na kallonta a tsaye , muryarta a sanyaye ta ce" Innata ciki?" Innarta ta fuske sosai, a maze ta ce" Ke kila wa kala ne" NADIRAH ta sake zuba mata ido, sai kuma ta kalli Auta Ta dan jima ta kalli wannan , ta kalli wancen, sai kuma ta juya ta nufi dakinta jiki ba karfi kwata kwata Tana shiga Inna Hindu ta zauna tana cire zumbulelen hijabin kashe su ta ajiye carbin a gefe tana sauke ajiyar zuciya sannan ta kalli Auta dake kasa tun faduwar nan ta ce" Taso mana autata, yar karama , yan matan Hindu gajera, zo nan" Daria ce ta kubucema Auta, a dan rarafe ta karasa dan kafafuwanta har kamar sun mutu ta zauna tana dora kanta a saman cinyar Inna Inna a hankali ta ce" Tabas ciki ne da ita, sai dai dan Allah ku kama bakunnanku, kar ku saki maganar nan ta fita yanzu, domin cikin bai wani yi kwari ba, kai ko kwarin ya yi ku barshi ya rayu a boye, idan Allah ya budi ido du mai son ganni da wandama baya so zai gani, ke kin san a inda Abanki yake, kin san su waye ke zagaye da shi ko?" Kuka ne ya kubucewa Auta, kuka mai tsuma zuciya, hakan ya saka ta rungume kafafuwan inna sosai tana zubar da hawaye A sanyaye ta ce" Alhamdulilah, ko yanzu raina ya bar gangar jikina na godema Allah Mamah, na godema Allah, na kuma tafi da farin cikin gannin lalle Ubangijina shine gagara misali, Mamah, na san Abah babu abinda zai iya yi maku na bacin rai a dangane da abinda ya faru, ku din masu farar zuciya ne, shi kuma ya san talaka da mai Kudi ko mai mulki duka bayi muke a wajen Allah, talaka futuk na iya samun rabauta fiye da sarkin da ya zalinci bayi, shi yasa yake addu'a tun karfinsa tunda sarauta ta zamo masa dole, kar Allah ya dora zalintar bayi a zuciyarsa, Allah ya shiga tsakaninsa da aikata haka......, Mamah yanzu yaya zan yi da farin ciki? Mamah ina son yin waya da ....... Ina son yin waya da ............" Sai kuma ta yi shiru tana lumshe idannuwanta, domin sai ta ji matsananciyar kunyar kiran mijinta mijinta a gaban Maman, sannan bata saba kama sunnansa ba ko kadan Inna Hindu dake share nata hawayen, muryarta a shake ainun , tana cikin yannayi ne na tashin hankali da kuma farin ciki, ita da kanta bata gane cikin Nadirah ba sai yanzu, emotion biyu sun hade mata, wani irin farin cikin hakan , domin a gidansu zata iya cewa Nadirah ce kawai ta yi dacen daga shiga sai dauka, mamantama sai da shekaru suka ja ta samu cikinta, bale ita gata cikinma bai samu ba, ama ga y'arta nan Allah ya kawo, wannan farin ciki dole ta yi ta ibada tana godewa mai sama, sai kuma tashin hankalin inda yar uwarta da mijinta suke, tabas wannan din shi zai fi disashe komai, sai fatan Allah ya bayana mata su A sanyaye ta ce" Auta?, Shin wai me yasa mijinki ko a leke ba'a ganninsa? Ba shi babu danginsa? Menene ya sa ya barki ke daya a wajen nan baya zuwa ba kuma ya kira?" Da farko shiru ne ya gabata a wajen, sai kuma a hankali Auta ta shiga magana kamar haka" To mamah yaya zai yi?, Da farko ya so daukeni mu gudu a lokacin da Umma kadai ce ta yi maganar kar ya kuma kirana ko a waya sai na samu lafia, sai kuma ABAHNA ya shiga maganar, domin Umma ta same shi ta nuna masa cewar dole fa sai an zabi daya, ko a barni tare da shi kulun in ringa kukan ni Abahna zan dawo, ni a kawo ni wajen Abahna, ni meye meye, ko kuma a kawo ni gefen Abahna ya hadani da likitoci a nema min magani , Abahna ya nuan ai bai ga hadin dan ina gannin mijina ko muna waya da shi ya zama matsala ba, mahaifiyarsa kanta ta tako da mahaifinsa kan maganar, a ranar Abahna ya yi tafia, Umma ta bugar da ni , sun ganni a matsayin mahaukaciya tuburan, domin shi mai gidan nawa yace sosai hankalinsu ya tashi, Umma ta hada baki da likita ya nunawa Abana dole sai an nisantani da shi mijin nawa in ba haka ba aiki ne zai ringa komawa baya, domin ba zan daina raba hankalina ba, a dole ya nemi zama da su baki daya ya gabatar masu da damuwar, ya nuna masu cewar ba zai tauye mijin nawa ba, yana iya karra aure ko ya sawaka min, duka dai abinda ba zai takura ba zai yi, shi ya nuna aa ba zai sakeni ba, ama iyayensa sun nuna dole fa sai ya yi aure, Mamah ina ji ina gani Umma ke kawo min komai na rahoton aurensa, aka yi ya tare da matar, shekara biyu ta nemi saki , wai ba zata iya ba tana rayuwa da mutun ama gangar jikinsa ta aura, ko hira take so da shi ta yi tsayi to fa sai idan maganata zata dauko, idan tana son gannin kyautatawa daga gareshi ta kyautata min, gidanta ko'ina kayana ne da hotunana , dakin mijinta hotunana, karshe dai tace ba zata iya ba, daga nan dai mahaifiyarsama ta daina zuwa, ban san dalili ba, a da takan leko lokaci zuwa lokaci, kuma du idan zata zo sai ta sanar hakan ke sakawa Umma ke makar da ni ta tsoratani, du zuwan da zata yi abinda zata tarar ya gyasa wanda ta bari...............sauki sai na Allah, a dole ta yarda na haukace, abin takaicinta danta ya ki rayuwar wani auren da wata........................" Idannuwan Umma a rintse, cike da takaicin wata rayuwar, a sanyaye ta ce" To ke, me yasa kika zabi zuwa nan ki zauna bayan idan kina tare da mijinki duk rintsi zaki tsalake wata fitinar?" Jajayan idannuwanta ta dago ta kalli Fuskar inna, hawayen dake diga a fuskarta ya sakata sauke ajiyar zuciya a hankali ta shiga share mata, a sanyaye ta ce" Mamah, a gabana Umma ke zuba magani a madarar Abana, sanadiyar zamana a gefensa kuwa sau bakwai ina zubar da abincin da ta zuba guba a ciki, domin wani lokacin nakan tayar da haukan karya na barar da shi, wani lokacin kuwa nakan yi summar karya ta yadda ba zai iya duban abincin ba, da addu'a da komai Allah ya sa bai ci ba, Mamah, na san ban isa na hanna ba, ama a lokacin gani nake yi ifan na matsa komai tana iya yi, har ta gane da gangan nake hanna masa ci ta tsoratar da ni da maganar mugun aikin nan da take yi, tace na jawa kaina zama a masarautar har na tsufa, kuma ta yi alkawarin idan na yi gigin sanar da maganar zata bugar da ni ta min sharin madigo, Abahna zai jefeni da kansa, shi kuwa ciwon abin ya kashe shi..............."............. Ta idasa tana mai fashewa da matsanancin kuka, kuka na samun sasaucin nauyin dake zuciyarta, tana jin yadda jikin Inna ke rawa na bacin rai, tana kuma gannin yadfa take hanna kanta sakin kukan itama mai karfi Zuciyarta cike da zafi da kunna a sanyaye ainun ta ce" Allah zai saka maki, Allah zai sakawa Yayanki, ba ku kadai ba Allah zai saka mana muma da ta sako mu a layin ta'adanci, Allah zai sakawa du wani wanda ta cutar, koda ta samu tsiratar da kanta a wannan karron zata hadu da nata gamon , domin tana wasa da hakin da Allah baya yafewa, hakin wani a kanka Allah baya gafarta shi, idan kuwa sakankancewarta ya saka bata gane furfurar kanta da janyewar fatarta da da yanzu ba lalle a kireta mahaukaciya, bata da hankali, ta kuma tabe, wannan mata na ajiye makaman fadana da ita, wannan mata Allah ne zai yi maganinta, wannan mata bama tunanin mutuwama zata zamo mata aya, irinsu su rayu sunna gannin rayuwar ta zame masu ukuba ya fi, irinsu ya dace su jima sunna kallon lamarin ubangiji gannin idannuwansu, wannan mata sai ciwo ya koya mata hankali, wannan mata sai tsufa ya koya mata hankali, Allah ya sa wannan mata ta maimaita shekarun da ta yi a duniya sau biyyar ta yadda zata ringa ihun kiran mutuwa da tunanin shin ita mutuwar ta manta ne?, Ta yadda zata bar duniyar da abinda take cikinta ba tare da ta mutu ba! Tabas wannan matar la'ananiya ce wace bata jin tsoron Allah, munafuka ce ita kuma azaluma ce, ki yi hakuri AUTA, ko me ta yi maki Allah zai warware maki kin ji?" Sosai Auta ta ji sanyi a zuciyarta, sosai ta ji bakinta ya bude, har zuciyarta ta cika da mamakin dama itama zata iya bude baki ta saki damuwarta haka wani ya saurara? Kusan a nan suka wuni, abinci da sallah ke tashinsu, kiri kiri NADIRAH kuwa ta labe a daki ta ki fitowa, da farko kuka ta sha da tunane tunanen da ba zasu gyarata ba, daga baya ta rike carbi tana Adu'ar Allah ya bayana mata iyayenta cikin aminci da lafiya, in sha Allah zata zauna da shi idan ya nemeta dan ta ji yaya za'a yi ya barta ta je neman iyayenta, domin ba zata iya zama bata neme su ba fa, sai dai ya yi hakuri idan ta gansu ya yanke hukuncin dake gyara shi a kanta! A bangarensama, sun cika dare sosai da SHEIK a bangarensa, domin a dawowarsu kusan magariba sai da ya bada damar shigowar UMMA , wace kana kallonta zaka ga bata tare da nutsuwa ko kadan, a yanzu ta saka alkyabar ama gaba daya tamkar an tonota daga cikin rami, domin kana ganninta zaka ga tsantsar tashin hankali da firgici a tatare da ita Sosai ta gabatar da rainin wayonta, da su koke koken yanzu yaya za'a yi ba'a ga bafansa da gimbiya ba, shima ya nuna mata tsantsar tashin hankali da sheda mata yanzuma daga Tanut din suke an baza dukkan jami'an tsaro ana nemansa, sannan an dora Huzaifa kujera kafin a ganshi A nan mamaki da tarin tambayoyi suka so zautata, me ya kawo HUZAIFA SOJA saman karagar mulki bayan ga ya'yansa maza manya? Ita fa, haukacewar da ta kusan yi wai jin an sace su, waye ya sace su? Ina suke? Ta zata abin wasa ne kamar yadda suka tsara ne sai ta nemi wayoyinsu ta rasa, karshema baban yaronsa ya sheda mata hankali tashe cewar an fa sace su, kamar ledar piya wata jama'a?, Mutane uku rigis kuma ba'a ga wanda ya dauke su ba? A haka ta koma tana tsantsamce da kowa, domin tana tafe tana waige waige da kame kanta dan kar aje itama a ritsa da itan, wanda ya sace sarki da matarsa da yarsa ta yiwu harda ita a layi, tana shiga bangarenta ta garkame ta kori kowa, sai a lokacin ta yi arba da madarar UMUGHLUK ITIBEL, wace ta yi baki kirin sakamakon maganin gubar da ta sauye baki daya Hankalinta ne ya sake tashi, ta je garin neman rarumar jug din ta barar da shi ya fadi kasa, ji kake tartsatsa ya fashe gaba daya madarar da maganin suka bare nan kasa A wajen ta zauna tana hade jikinta tamkar wata karamar yarinta tana yarfe hannayenta bayan ta tuge dan kwalin kanta tana ta wani abu kamar sabin kamu a rikice gaba dayanta ta ce" Na shiga uku, na barar da maganin gana daya, yanzu wa zai samo min wani?, Kai kuma dan Allah ka taimaka ka kirayeni ka ce min kun buyan ne ya sa ake tunanin sace ku aka yi, idan ba haka ba ina zan shiga da faduwar gaba da tsoro a cikin masarauta?, Waye ya sace ku? Me kuka yi masa? Idan ASADEEK ya gane ba ku kuka haifi wancen yar banzar ba yana iya tisoni a gaba fa?, Idan ya tambayeni me zan ce masa bayan ya san na san yarku? Wayo na shiga uku menene wannan tashin hankalin dake nufo ni, komai na kasa ganewa gaba daya komai sai shige min yake yi a cikin junna?, Wayo na shiga uku ..................." Da wannan suka cika dare shi da SHEIK sunna sake tataunawa a kan hanyoyin da zai bilowa wasu abubuwan *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣1️⃣ Sai kusan karfe tara da wani abu SHEIK ya tafi, shima ba dan sun gama ba, sai dan su hau kan tsarinsu na gaba, wanda SHEIK din ne zai gabatar da binciken lokacin da zasu iya dauke babbar jakadiyarta a kwana kusa, dan basa so a firgicinta da faduwar gabanta ta samu sasauci ko na second daya Alwallah ya daura bayan ya yi wanka ya haye salaya, so yake yi zuciyarsa ta yi sanyi, so yake yi ya samu nutsuwa irin wace babu wanda ya isa ya bashi sai ubangijinsa Sai da ya kai kusan karfe biyun dare yana ibada, sannan ya mike ya karasa wajen kwonciyarsa, ya yi adu'ar barci ya kwonta yana rungume hannayensa a samn kirjinsa, a sanyaye ya lumshe idannuwansa yana jin nutsuwa da sabon tunani a kan matsalolinsa sunna ta shiga kwakwaluwarsa, a cikin tarin dacin da yake ciki sai ya ringa hango sauki , saukin nan kuwa ba komai bane face wani haske da ya shigo kwakwaluwarsa, hakan ya saka shi sakin dan murmushi yana jin abin har cen kasan zuciyarsa, har kamar abin na son ya saka shi jin babu dadi dan baya gefensa, ba komau bane face NADIRAH, zai iya cewa gwadama da suka bashi mace a lokacin da baya tunanin samu....... Zai iya cewa gwadama da suka cenza masa da Soul mai daraja, daya tak da bai hado irinta a kusa ba, idannuwansa ya lumshe a saman lebensa kadan kadan ya ce" TUZURUWAR kauye, ya dace a bar maraya ya huta, tunda ba za'a zo inda nake ba............a bar tunanina ya huta ko?"..................................................... Cike da begen nan a kasan zuciyarsa ya samu barci mai dadi, mai kuma nauyi, dan kuwa sai da kiran sallah kusan karewa ya jiyo a kunnayensa ____________________________________ Washe gari A ranar wunin da aka yi, an yi shi ne cikin tarin taro na jama'a, ya wuni a fada ne cirrrrrr ba sasautawa, domin baki ya ringa samu ta ko'ina masu tafe da son sannin maganar da ake shelawa ko gaskiya ce?, Da jajantawa, asalima sakonsa na aiken da ya yiwa sarkin yanka sai da yamma suka kadaice ya sanar masa , sannan ya samu ya sake fita ta sirri ya je ya ga bakinsa da ya kilace idan har sun fara gane sun shiga uku ko da saura? Ai kam ya tarar da su ba yadfa suke, madubi ne da shi yana iya ganninsu tar tar, su kuwa basa gannin komai, a lokacin da ya je ya same su Bahija na zaune tana kallon waje daya, fuskarta ta yi jajajir tamkar wace ta sha duka, ita kuma kuka ne ta sha kamar ba gobe, iyayenta kuwa mahaifinta yana tsaye yana ta kallon wutacen dakin, ita kuma mahaifiyarta tana kwonce ta dukunkune cikin alkyabart , ga dukkan alamu ita rashin shayin tuni ya fara kaita makura Bai ce komai ba ya yi tafiyarsa bayan ya sheda masu kar su rasa abinci ko abin sha, shayi kawai za'a hanna masu Yana komawa bangarensa ya tarar da tsare tsare irin na mata masu daraja, Watau aiki irin na mace mai kishin mijinta An cenza masa su cafet labulaye, komai dai hajia uwar gida ran gida mai girma HUZNAH abincin ruhinsa tana kai kawo sai baza kanshi take yi ta kuma dauki kwaliya daidai gwargwado, duda tana fama da kayan alkyaba, ama kuma tsarin shigarta dake kasa tamatukar kawatar da idannuwansa ta tarbe shi da kula da kauna ta rakashi har dakinsa sannan ta koma falo cike da farin ciki, a zuciyarta tana ayyana ko me take tunani ta fi ta, domin ba zata taba gwada mata kula da mijinta ba, zata ga aikin soyaya ba nata na shirme ba, za kuma ta ga ko tana yar uwarsa ita din ta fita tunda soyaya ce tsakaninsu da aminci, du abinta bakuwa take a cikinsu ta yi biyaya ko ta gaza gane komai, ita dai babu Wanda ya isa ya fit sannin wanene mijinta! Koda ya sauko cin abinci ya ringa binta ne da kallo mai cike da tausayi da tausasawa A lokacin da take zuba masa abincin da ta bata lokaci tana daahuwarsa , a tausashe ya dora hannunsa saman nata ya sakar mata da murmushi a hankali ya ce" Ya isa haka HUZNAH ko so kike na gaza barci ciki ya cika sosai?" Murmushin ta sakar masa itama tana sada kanta, a nutse ta ce" Allah ya taimakeka, idan ka gaza yin barci ai na bani, gwara na bari haka din" Abincinsu suka ci hankali kwonce, saima da suka kusan gamawa ne , bayan shi ya gama tuni, yana dan shan madara yana dan kallonta ya samu kansa da sakin murmushi, fadansu ita da NADIRAH ba zai taba daina bashi dariya ba, shi kam gaskiya bai san ko aikin shedan ne, ko menene? Sai ya ji fadan nasu ya matukar kayatar da shi, in dai irin fadan nan ne su yi ta yi yana tsakiya yana murmushi abinsa, shima namiji ne kishi ne ake yi a kansa, ya isa ne wai, a hankali ya ce" Bakya yin missing din Auta a diner?" Abincin da bata gama ci ba ta dan dakata, sai ta samu kanta da tauna maganar a ranta, to ama a kan me zata yi missing din wace bata girmamata, ai Auta bata wani dauketa da daraja ba, gayanan ana yi mata kishiya ta je ta dinke da ita wai harda kwana a bangarenta , ita zata nunawa dangi? Ai dadin abin itama ba daga sama akaa cilota ba, tana da nata dangin , babu wanda zai wulakantata saboda haka A bayane kuwa sai ta yi murmushi ta ce" Ni raboka da Auta ai yau kwana uku, tana bangarensu" Dan tsai ya yi, sai kuma ya kawar da maganar daga ransa, domin da farko sai ya ji kamar ba dadi a ransa, Auta ce fa, mai sunnan Maman Aba fa, ko me yasa sam HUZNAH bata damu da kowa nasa ba in ba shi kadai ba, ba ruwanta da kowa nasa sai shi kadai tak, ko mtan Sheik bata zumunci da kowa, ko me yasa? Ita danginta kadai take mu'amala da su, summa basa wani ziyartar junna in ba ta yi dalili ba, ko dan sunna aure da sarakunna ne? To ma shi zumunci ai ba'a ce banda matan manya ko manya ba, du wanda bayaa zumunci ai baima ji dadin rayuwarsa ba sam Yana kai dubansa kan kujerar Nadirah ya samu kansa da sakin murmushi, rabonsa dai da ita tun jiya daa safe, ko a wulge ba'a leko shi ba, da ace wani abinta ya tsumkota, ko yan nemna rigimarta sun tsumkota da yanzu ka ganta ta yiwu zani daban, riga daban ta zo ta gabatar da neman rigimarta ta karra gaba, wai idan zata gaishe da jama'a sai tace sasanunku, uhum bai taba gannin gidan rikici irin yarinyar ba sam, abinda tun randa ta fara ganninsa bata jin tsoronsa bale yanzu da mata suka ga maza? Ai sai dai a kokarta a ji tsoron Allah kar a raina mazan kawai☹️ Sun dan jima a falon kasa sannan suka haye sama, A daren ya so fara yi mata sharan shanye, sai dai gaba daya ya ji raunin hakan a zuciyarsa, a dole ya yi shiru da bakinsa ya shiga gabatar da sallah har sai da ya tabatar ta yi barci sannan ya haye sman gadon gefenta ya kwonta yana binta da kallo Kai in kuwa hakane, gaskiya an cuceta, ga dai mace fa, sai dai an shiga tsakani, an hanna mata jun dadi bale shi Dole ya ji tausayin HUZNAH, dole kuma ya taimaketa, dole ya tayata neman hanyar da zata bila *___________* Ranar biyun kwananta Kasancewar yanzu itama takan hantse ne a bangaren mijinta, yauma tana zaune saman kujera mai zaman mutun daya, mai laushi tana binsa da kallo, a lokacin da yake dan kawonsa a cikin dakin barcinsu hannunsa daya a bayansa a jimke, dayan kuwa a mike a kusan kunnensa yana amsa kira, da yannayin da ta fahimci kamar an dan sosa ransa, sai dai a nutse yake bayanin da ta kasa gane wani yare yake yi, domin ba larabci bane, ba kuma turanci bane, ba buzanci bane, ba kuma hausa bane, har ya gamaa ya kashe kiran ya dan jefa wayar saman bed dinsa dake gyare da shinfidar da suka kwana sama wace shine ya jaja da hannunsa ya gyara dan HUZNAH kam bata san wannan yaren ba, sanna ya juyo inda ya saka ta zauna dan zai tatauna da ita A nutse ya janyo kujerar dake gefe ya ajiye face da ita sannan ya hau ya zauna yana mai hade hannayensa ya zubawa fuskarta ido, wace hakan ya sakata sada nata idannuwan dan sun mata kaifi a cikin natan Dan gyara zamansa ya yi yana kallon agogo, a hankali ya ce" HUZNAH, wata tambaya ce da ni kuwa, ban sani ba ko zaki iya tuna a lokacin da kike amarya, me da me ya faru?" Kanta ta dago da alamar tambayar bata gane ba Dan murmushi ya yi ya ce" Oh sorry, ina son sannin a lokacin da aka kawo ki gidan nan, da wa da wa kika mu'amalanta? Wa da ya maki kyauta? Me da me aka baki? Waye mai maki dahuwa?, Wa yake kula da harkar tsaftar bngarenki, komai da komai dai" Da alamu na ta fara damuwa ta ce" SULTAN, wani abu ke faruwa ne?" Gefe ya kalla kadan, sai kuam ya sake dubanta, bai ce mata komai ba yana kallonta, watau dai amsa yake so kawai Zama ta gyara a hankali ta shiga tunani, maganar shekara goma ce fa yake yi mata kai tsayen nan? To ita wasun a lokacin da ko kallonsu bata iya yi dan kunya da bakunta da kuma mutunta su? Abu daya zata iya tunawa tunda aka kawota gidan a matsayin bakuwa A nutse ta fuskance shi ta ce" Aban AUTA, a lokacin da na zo gidan nan bakunta mun zo da jama'ar fada ne, a kala sun min sati biyu har sai da Abah yace ya isa hakanan maza su dawo gida, abinda nake tune da shi dai a lokacin da nake da bakunta komai nawa a wajen UMMA ne, kama daga abincina, suturuna wa'inda aka ringa nuna min kafin a kawo ni bakunta bangarenka, har zuwa shirye shirye irin na amare da ake kara yi a lokacin, wanda a wannan lokacin ban ga an yiwa BAHIJA ba" Idannuwansa yake dan kiftawa bayan ta ajiye maganar A nutse ya sake fuskantarta , da hannunsa na dama yana dan misaltawa ya ce" Ohk, a cikin launikan abincin da ake baki, ko sutura, ba'a baki abinda ya saka kika tsantsamta ba?, Koma menene ba'a baki wani abin da ya saka kika dan yi mamakin abin ba? Ko sutura baki yi anfani da wata wace sam baki yarda da ita ba?" Fuskarta na nuna alamun damuwa ta ce" Allah ya taimakeka, hankalina ya fara tashi da maganar nan, shin akoy wani abin da yake faruwa ne dan Allah?" "Kima tune ko bakya tune da komai?" Ya sake fada kai tsaye yana kallonta Ksa ta sada dubanta, gaba daya kanta ya fara sarawa dan neman abinda ya saka shi yi mata tambaya irin wannan, gaba daya ta nemi amsar da ya dace ta bashi ta rasa tunda ita bata ga dalilin tambayar tasa bamaa kwata kwata A tunaninta bata hango wani abu da aka bata ta ci, ko ta saka a jikinta ba, wanda zai sakata a wani irin yannayi? Ta rasa gane gabanta bale bayanta, gashi sai magana yake bata a dunkule A sanyaye ta dago tana kallon kamilaliyar fuskarsa, ba zata ce tana karantar bacin rai a fuskarsa ba, duda ta yi mamakin yadda sam yau bai tashi da muguwar damuwar ya kasa shigarta ba, hasalima bai gwada shigar tata ba, ita dai ya taimakawa ya rikitata har ta samu nutsuwa, ama shi sai ya yi kwonciyarsa yana rungumeta a jikinsa, ta yi tunanin zasu farka daa ciwonsa ne , sai ta ga ya tashi y shige bayi ya samu sallat asubahi, har gashi da ya shigo sun dora hira Ajiyar zuciya ta sauke a sanyaye ta ce" Ni dai a tunanina, bana tune da wani abin da aka bani wanda ya sakani a wani yannayi, duda ban fahimci wani irin yannayi kake nufi ba,ama sam ni ban ga wani abin da aka bani wanda ya sakani a shaku ko hali na rashin lafiya" Idannuwansa ya lumshe, a hankali ya kai hannunsa saman llalausan sajensa yana shafawa Kasa kasaa ya ce" thn, kina iya tafiya " *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣2️⃣ Kallonsa take yi kamar zata dauke shi da idannuwanta, Jiki babu karfi ta mike tsaye tana gyara alkyabarta, sai kuma ta sake juyowa tana kallonsa fuskarta na raunana A sanyaye ta ce" In tafi?, Shikenan ba zaka sanar min wani irin yannayi kake nufi ba?" Idannuwansa da sam kwanakin nan basa rabo da dan jaja jaja ya sauke a kan fuskarta Mikewa ya yi tsayen shima, hakan ya sa tsayinsa kere nata sosai Yana kallonta ta kasan idannuwansa, muryarsa na fita a azance ya ce" Ban san me zan ce ba HUZNAH, ban san wani irin yannayi zan kirayi abin ba, abinda na sani shine damuwar dake damunmu tsayin shekaru goma a jikinki ne take ba a jikina ba" A rarabe ya ajiye maganar, sannan a lokacin da ya ajiye din kwayar idannuwansa mararsa tsoro sai da suka kauce daga cikin nata dan jin nauyin furucin, hakan ya sakata tsure jayen lebunansa da ido tana son gane me yake nufi bata ko kiftawa A hankali ta ringa jin faduwar gabanta na dan son ta fi karfinta Da sauri ta ture tunanin dake cikin zuciiyarta ta hanyar dan yin dan murmushi tana kallonsa a hankali ta ce" Cutar dake damunmu? Wace cuta ce wannan............................" Sai kuma ta dakatar da furucinta, a hankali ta dago idannuwanta ta saka a cikin nasa domin ya dake juyowa ne yana kallonta Irin kallon da yake yi mata ya sakata saurin bude bakinta dake dan barbarbar yana rawa kamar mazari , sai kuma ta mayar da shi ta damke shi, ama kuma hannayenta ne suka amshi rawa a hankali a hankali har ta dago su tana kallo, Shima hannayen nata yake kallo zuciyarsa na neman babalewa dan bai san ta yaya zai iya dogon magana da ita a haka ba Yanzu fuskarta ba alamun murmushin dazu , ta sake dubansa ido cikin ido , muryarta na crakng ta ce" Husband......., Kan nufin cutar dake damunmu, wace ta hanna mana kasancewa daya, wace muke zaune cikin kunci sanadiyarta......a jikina take? Like a jikina kadai ne kake haduwa da hakan?" Dara daran idannuwansa ya sake saukewa a kanta, tarin rauni da duba irin na nagarta yake yi mata, hakan ya sakata jin zuciyarta ta yi bugawar da tana da hawan jini ta tabata da a yau sai ta tashi da shanyewar barin jiki A hankali ta damki damtsen hannunsa sakamakon tareta da ya yi a lokacin da ta ji kamar za'a makata da kas sanadiyyar Juwa Tun daga kafarsa ta ringa dago dubanta a hankali har ta kawo kan fafadan kirjinsa, zuwa zaratan hannayensa ta sauke a kan ni'imtaciyar fuskarsa mai sakata karra jin du duniya babu macen da ta kaita dacen santalelen gaye a rayuwa Muryarta cen ciki ta ce" Yaya aka yi ka gane ?" Bai ce mata komai ba, sai dauketa da ya yi cimak ya nufi bakin bed da ita ya ajiyeta sannan ya tsaya yana harde hannayensa yana kallonta ya ce" Ba wannan ne maganar da ya dace ki tambayeni ba, abinda nake son sani ta yaya hakan ya same ki dan mu nemi magani, HUZNAH mu ba kannanun yara bane da zamu tsaya kan wannan yar maganar mu dagawa junna hankali, inaga a yanzu kin yi girman da ilimin da zaki kaucewa hakan......, Ki dan yi abinda ya fi armashi shine yin nazarin tambayoyina dan na samo mana magani!" Ta yaya zata iya hanna kanta fashewa da kuka, a dole ta yi kuka, a dole ne ta yi kuka idanma ana yin na jinni a yau ita kam zata yi Cikin matsanancin kukan da ya sarketa ta zuba masa rinnanun idannuwanta, yanzu mijinta? Abin kaunarta, abin tattalinta, mafarkinta ne wata ta malaka ba ita ba? Har yake nuna karamin abu ne? Ilimin me? Girma? A gingunemiyar uwa yake kallonta kennan? Shi yasa yake iya tsayawa yace da ita ta yi girman da ba zata iya yin kishinsa ba ko me? Muryarta na fita a hargitse cike da dacin kalmar dake fita a bakinta ta ce" Yaya zaka yi magana da ni a kan abinda ya shafeka ka auna ni a dandaja? Ilimi? Girma? Na yi maka tsufan da kake tunanin zan iya kawar da maganar nan a kiftawa da bismillah?, Innalilahi wa inna ilaihi rajune, a jikina? A ina na hadu da wannan masifar? A ina na hadu da wannan balakin?, Yaushe hakan ta sameni? Na tabata tun kafin ka fara yi min duban mace ce ni da neman samun nutsuwa a jikina na hadu da shi domin a darenmu na farkoma a asibiti ka waye shi dan tarin cutar da ta dunkule maka a mara ka kasa fitarwa, ashe tun lokacin nice rashin lafiyar nake tunanin ina zaune da kai dan soyaya ba zan iya barinka ba koda kuwa baka iya anfanar min abinda kowace mace ke anfanuwa da shi? Wayo Allahna! Na shiga uku, ita ka samu ka shigeta ama ni aa? Ita da ta zo jiya jiya ce ta samu wannan mukami ni kuma aa? A dole ta ringa yi min gani gani, a dole tace min kar na saki na zo idan kun a soyayarku, a dole ka yarda da dukkan furucinta dan ka fi sonta, to ta yayama za'a hada soyayata da tata bayan ita tana iya baka abinda ni ba zan iya baka ba, ta yiwuma itace ta gamani da cutar nan ba kow.......... "h HUZNAH!" ASADEEK ya fada a kausashe, muryarsa da dan karfi, idannuwansa gaba daya a ware a saman fuskarta cike da mamaki yana kallonta HUZNAH dake kuka harda majina da hawaye hannayenta bibiyu a saman kanta ta tuje gashin kanta ta bale abin alkyabarta tana jan kasa daga jikinta ta dauko dubanta a raunane ainun ta sauke a saman kansa A hankali ya miko hannayensa bayan ya sauke raunaniyar ajiyar zuciya yana kallonta, muryarsa a sanyaye ainun ya ce" Haba HUZNAH, maimakun mu yi maganar da zata fishemu,, mu samu mafitar da zata gyara mu, sai ki dauke maganar ki zubata gaba daya kan abu guda daya tak?, Haba HUZNAH................" Ya dakatar a hankali yana sake kallonta sannan ya ja numfashi kadan ya ce" HUZNAH rayuwar shekara goma fa ba ta kwana goma bace, kuma a yau idan a kaina abin yake zan fi so na sani dan na magance ko dan na nuna bajintata a gabanki ko?, HUZNAH yaya zaki kawo maganar soyaya ta wannan fannin kamar ita kadai ce rayuwar auren? Da ace shi kadai ke iya rike aure da mun jima da raba hannun junna HUZNAH, idan hankali ya tashi ai hankali yake nutsar da shi, kin san tun yaushe nake son na tuntube ki a kan hakan? Kar ki sako magangannun NADIRAH a matsayin wani abin, yarinya ce, kar ki ga laifinta kin ji?, Dan Allah ki sasauta min hankalina a tashe yake fa, kin ga abubuwa sun min yaw yanzu sosai HUZNAH" Kwarai, idan hankalinka a tashe, komai ganninsa kake yi ba wai, dukkan furucin ASADEEK sai suka ringa zuwar mata a karkace, gaba daya duniyar ta fitar mata a rai a lokacin da zuciyarta ta gama sheda mata hakane mana, dole ne yace damuwa ta masa yawa, a yanzu ai basshi da wata damuwar da ta wuce ta gidan hutunsa, dole yace tata damuwar ta biyo baya tunda yana cikin damuwar an sace iyayen matarsa, yana magana da cewa ko NADIRA ko wace? Wacece Nadirar kuma?, Kwata kwata a yanzu idannuwanta banda bakin kowa ciki harda shi babu abinda take gani Hannun nasa ta kasa kamawa, da kyar ta iya mikar da kanta, a tsayin shekaru goma da suka yi basu taba samun sabani irin na yau ba, basuma taba samun magana mai ciwo irin ta yau ba, damuwarsu kanta basa zurfafa tunani a kanta dan basu da maganinta kuma basu dora tarayarsu a kanta ba, a yanzu dole ta ji ta rikice, dole ta ji tana neman shiga uku Tana kallonsa Muryarta na rawa ta ce" Koda baka so, dole na fada, a bayane yake a zuwanta gidan nan na hadu da dukkan damuwar duniya, ni da ita sai dai Allah ya saka min!, Maganar sonta kuwa, ka san ka fi sonta da ni, a bayane yake, takan tsaya ido cikin ido ta yi maka rashin kunya, sai dai ka ringa murmushi , karshe yau ka kirayi lamarin da yarinta, a ina yarintar? Yaan magana sun ce SO hanna gannin laifi ne......., Dan Allah ka bani dama na je Baban gida dan a nema min maganin abinda ban san da shi ba sai da matar so ta zo!" Idannuwansa ya rintse, soai yake yi mata uzuri domin abu ne da dole ya girgiza zuciiyarta, ama kuma ya yi mamakin saurin gazawarta da saurin yanke hukuncinta, to ita tama rasa a me zata tsaya ne ai, da bakinta tace a washe garin tarewarsuma ya tashi da ciwon, sannan tace ba wanda ya dora mata sai NADIRAH, shi a ganninsa idan aka ce shine a jikinsa zai zauna ne ya yi ta bincikar kansa har ya gano mafita, ama ita ta ki a yi haka, karshema ta bige da abubuwa kamar wata yarinya karama? Juyawa ya yi ya nufi wajen kayansa ya bude ya zubawa kayan kallo gaba daya ya rasa kayan yake kallo ko kukan da take shekawa ke hanna masa motsin kirki? Kukanta take yi bilhaki, ta ci gaba da magangannunta, cewa take yi ba zai ce komai ba? Tana jiran amanarsa ne na ta tafi gida, watau gidan iyayenta a nema mata magani, maganin da ta kasa bashi amsar da yake tambaya dan ya sama masu mafita, maganin da a yanzu ya sani yake kuma neman makarin abin, gaba daya ta juyar da maganar ta kasa sauraronsa, cen kasan zuciyarsa sai ya ringa jin muguwar kewa, da son zantawa da wani na jinninsa, sosai kewa irin ta iyaye ta ringa mintsininsa Yana sauraronta har ta gama ta fice da kukanta cewar ai shikenan tunda yanzu ya samu mace ita kam da take hoto ai sai a kara mayar da ita gefe dan kar ta tsare hanya Idannuwansa dake lumshe ya bude ya bi kofar da ta fice da kallo, kkasa kasa ya samu kansa da furta" Uhum" a cikin zuciyarsa kuwa yana girmama girma da karfi irin na mace, wanda ba zata daukeka ta makaka da hannayenta a kasa ba, ama Allah ya bata damar da zata iya yi maka sal komai girmanka da jama'a suke gani ta sileka tsaf ba ko kunya da tsoron Allah, Lalausar shada ya zarro mai ruwan hanta, dinki ne mai gari da yar ciki, kusan du dinkunnansa haka suke dan ba kasafai zai saka dinki simple ba sai irin in zai yi fitar sirri Bai saka garin ba, rigar da wandon kadai ya saka ya dauko hular kayan da Mancheste ya balla , Hular kuwa ya riketa a hannunsa ya karasa wajen turarukansa ya yiwa jikinsa barin turaren sannan ya koma wajen takalmansa ya sakka , ya karasa wajen comand na AC ya dauka ya kashe su biyun dake dakin ya kuma kashe light din Bai baro dakin ba sai da ya cire soket din da aka jona na turaran wuta sannan ya janyo kofar ya rufe da Ky dinsa ya fice da shi, sabon abinda ya tsira kennan, a yanzu baya barin Ky dinsa ko dan rashin yardar da aka haifar masa a zuciyarsa Tafe yake a hankali har ya karaso kofar dakin ta baya ya dakata yana kallo, Wayarsa ya ciro ya shiga kiran number SHEIK *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣3️⃣ Wayarsa ya ciro ya shiga kiran Number SHEIK Bata jima tana ringing ba ya daga A nutse ya sanar masa cewa yau za'a dauke yarinyar karfe biyu na rana, domin a lokacin take daukan doguwar hanyar dake kaita bangaren da mahaifiyarta take dan amso kule kulensu na munafurci Ya gamsu da hakan ya katse kiran sannan ya yi anfani da Ky din wajen ya bude ya shiga ta ciki ya rufo ya mayar da shi aljihunsa sai kuma ya ringa tahowa a hankali yana saurarawa dan a sanninsa a wajen nan akoy matar dake iya zama sarakuwarsa, watau INNA HINDU Dariyar da kunnensa ke jiyowa da kuma hira hankali kwonce ya saka shi sake zuba idannuwansa a kanta, Auta hankalinta kwonce , dariya take yiwa Inna dake tambayar shin abinda ta yi mata kwontacen tuwo ne ko wani tashin hankali ne da galmi galmi a baki da kuma zakin madara, watau FLAN, fama take da Innar kan ta ci abinci , kwata kwata innar kwana biyu sai a hankali, ta cika damuwa a kan halin da yayarta take ciki, dan NADIRAH ba'a zancenta domin ita kiris take jira ta fashe da kuka ba kunyar kowa ta ringa haharba kafa tana fadin innar birni da aban birni Dan murmushi ya ji yana taso masa daga kasan zuciyarsa, sai kuma ya dan koma kasa kasa ya yi salama ta yadda ya tabata zasu iya jiyo shi Auta ce ta iya amsawa, inna kuwa ta nemi rikicewa a lokacin da ya bayana a gabansu ama ba wai ya shigo gaba dayansa bane, domin dakatawa ya yi yana kallon Auta da ta nufo shi fuskarta Kwonce da farin cikin ganninsa A daburce Inna ta nemi dukawa kasa gaba dayanta, ta jimke hannayenta kamar dai yadda ta yi farkon haduwarsu, bakinta na neman hade kalma da kalma ta ce " Barka da warhaka Uban marayu......" Sai kuma ta kai dubanta kan NADIRAH wace tunda suka yi ido hudu da shi gabanta ya yanke ya fadi ta sada kanta tana wasa da yan yatsunta biyu tana jin yadda idannuwanta ke marmarmar sunna kokowar su sai sun kubce sun kalle shi, gangar jikinta kuwa ya kwashi wani irin kaikayin da bata san ko na meye ba, zuciyarta kuwa ta ringa wani irin dokawa har zufa ta nemi tsatsafo mata a gaban goshinta, hakan ya saka ta lumshe ido tana jin wani hawaye mai dumi yana son tarun mata a cikin idannuwanta Inna kuwa nan da nan ta tuna da abinda suka aikata, su yan ta'ada, hakan ya saka hankalinta ya nemi tashi, kasa kasa sosai ta ce" Ke indi, kar dai hukuncin ne ya tardo mu yau laraba rana ta raba tsakiya gatse gatse za'a karmu ? Ba za'a yi hakuri a kaimu juma'a ba ko samu tsalakewaR tambayar kabari?" A hankali ya janye idannuwansa daga fuskar Auta dake ta doka masa murmushi ya dan saci kallon Inna, a kalamanta babu abinda bai ji ba domin ba wani kwaramniya a dakin, TVma a kashe take gaba dayanta Ba zato ya ji dariya na son fitowa daga bakinsa, a dole ya kai dubansa kan Auta ya ringa sakin dan murmushi mai sauti kadan sannan ya dauki wayar tasa ya latsa numbar Aban Birni ya karrta a kunnensa A tausashe ya amsa salamar da Aban birni ya yi masa, sannan ya ce" Barka da warhaka Abah, ya gida, ya ibada" Cike da jin kunya da mutunci Aban birni ya shiga gaishe shi, sai dai ASADEEK shima ya kasa amsa gaisuwar dan a ganninsa ta yi yawa, shine ya dace ya gaisar da shi haka, ama Abah ya gaza rage bashi girma har haka Dan murmushi ya yi ya mikawa Auta wayar yana fadin" ki kai masu wayar" Auta ba musu ta kawowa inna wayar wace ta yi tsuru tsuru baiwar Allah tana ta maimaita kalmatu shahada dan ta sabarwa harshe da fatan idan abin ya zo a fadeta dai-dai ta karbi wayar tana tambayar Aut waye? Sai dai Autar ta nuna itama bata sani ba, hakan ya sa Inna kara wayar a kunnenta a gajarce ta ce" Halo salama alaikum Hindu ce waye a ta dayan bangaren?" Yana yar daria ya ce" Ta habu makadi kike uwar Indi ja gabar dukiyar kasan gadon karfe mai komai dozin" Ido ta zarro, dan kuwa du duniya ta san mutun daya tak cilo yake yi mata irin kirarin nan face Aban birni, tsaye ta mike tana fadin" Ka rantse da Allah salihu ne? Wayo ni ta Habu maman Indi dama kana raye? Ina auntyn take dan girman Allah? Ina kuka shige? Kwai yana nan yana ta fashewa in fada maka Indi dai kafa ta kwasa ta je ta bude zare da abawa a gaban uban datawa, yanzu haka dai mu a hannu muke dumu dumu, ta yiwu a yanke hukunci yau......." Sai kuma ta shiga rike harshen zani tana fyace majina da hawaye ta ce" Ko a ina kuka buya ka sanarwa Habu ni na yafe masa, ya yiwa Allah ya yafe min yan yawace yawacen da yake hannani nake yi, ina yi ne dan na dan saku da zaman da gida da kuma yiwa maneman Indi da rigima kashedin kar su taba min Ya ka ji SALIHU?" Auta daria take yi bilhaki, ASADEEK kuwa jingina ya yi da garu ya kawar da kansa ya cije iya cijewa har sai da sansanyar muryarta ta ce" Innata wai Aban birni ne? Ce masa ga Indi bani shi mana " A hankali ya juyo ya zuba mata lumsasun idannuwansa Shigarta ba wata rikitaciya bace ba kuma mai kasaita bace, ama sai ta zama wata kasaitaciya a idannuwansa Tana matukar son atampa, domin sket ne da riga na atampa a jikinta dinkin gaba daya ya bi halitar jikinta ya kawata sai daukan idannuwansa take yi Hasken fatarta a cikin atampar mai ruwan ja ya matukar haskaka, harma kamar ta fi kulun haske ko dan ya kwana uku cir bai ganta ba? Dariyar da Inna ke yi tana rike karkadaf da wayar a kunnenta tana sake tambayar wai Fatime ce? Ta rantse da Allah itace , NADIRAH na ja tana ja ya saka shi a hankali ya sauke dubansa a kan Auta Murmushi ya saki yana kallon yadda Auta ke fara'a da fara'arsu , ta ce" Abahna ka raba rikicin cen fa, ba zata bata wayar nan ba, ka ga Mamah har ta dawo normal bayan kwana biyun nan ko abinci sai na yi da gaske take ci, bale Aunty sam take kin ci bayan yanzu bai dace ta ringa wasa da cikinta ba" Bai gane manufarta ba, abinda ya fi tsaye masa a rai sunnan da ta kirayi inna da shi, Mamah..................., Sunnan ya fito daga cen kasan zuciyarta ne, kuma a saman lebenta yana bada amo ne kamar idan D'a zai kirayi mahaifiyarsa Abinda Fatime ke sanar masu ya saka su zarro ido, sai kuma NADIRAH ta ringa tafa hannu ta juyo inda yake tsaye Sosai magana ke saman lebenta, so ta yi ta ce da ka san inda suke, kaine ka dauke su ama ka kyale ni?, Sai dai tanaa saka idannuwanta a cikin nasa ta samu bakinta da yin nauyi, zuciyarta da bugawa, sai kuma haushin irin yadda yake bambanci da nuna mata yana sin matarsa ya taso mata, hakan ya sa ta turo baki, hadi da galawa bangon da yake jingine Harara kasa kasa ta furta" masu mata ko mema aka zo yi min dakina?" Tsaf yake kallon lebenta, ta hakan ya gane furucin bakinta A dole ya idasa sakin murmushinsa ya ringa neman sai sun hada ido, har dai hirar ta Inna ta ki karewa ta shige ciki tana bada bayanin abinda ya faru dala dala , wayaa kuwa kamar tana yiwa na nesa kugi du ta ware murya tana bada labarin gaba daya ta manta wayarma ta waye kuma a gaban wa take, ita dai farin cikinta ya samu da ta ji ahalinta Shiru ne wajen ya dake dauka A hankali Auta ta janyo hannun yayanta har falon tana nuna masa wajen zama ta ce" Abah zauna bara na kawo maka juid din da muka yi ni da Aunty" Tana bada baya ya sake duban NADIRAH, wace ta yi saurin dauke nata idannuwan daga kansa, danma kar a wani ce kallon wani abin ne, kawai dai tana son gane kalar shadar jikinsa ne dan ta mata kyau a jikinsa sosai wollah, kamar majiya karfin filin din indiya Murmushi ya yi ya miko hannunsa kasa kasa ya ce" Momyn Auta, asalamu alaiki" Ido ta dan zarro, sai kuma ta dago ta zuba idannuwanta a saman hannun Da sauri ta kallo hanyar da Auta ta bi, sai kuma ta sake kallonsa, kasa kasa tana dan matsawa kadan ta ce" Ka mayar da hannunka fan Allah kar Auta ta gani ta min wata fasarar, ba kyau gaisawa da kato fa.............." Tahowar Auta ya saka NADIRAH saurin kara ja baya tana turo baki da kallon dariyar da ya faraa yi yana son dole sai ya bita sun yi musabaha , ita kuma tana neman labewa da sake bata fuska a dole ba zata gaisa da kato ba😌 Murmushi Auta ke yi, zuciyarta fara'a kamar zata fito ta fado daga kirjinta, sai kuma suka raka NADIRAH da kallo gaba dayansu dan a guje ta ruga ta nufi dakin da innarta ta shige tana haki Dariya Auta ta saka tana ajiye abubuwan da ta jero ta zauna tana fadin" Abah ka korar min Auntyna....." Shima fuskarsa yalwace da farin ciki ya ce" Ba ta hannaki cewa aunty ba? Momy ce fa?" Ai kam Auta ta kara saka yar daria tana cewa" Abah, ai idan na ce maka aba ne take kishi, sai tace bafa ta sin bambanci, haka tace Abahna sam bata tunanin idan yana tsoron Allah, wai sai ya kirayi matarsaa a wani sanyaye ita kuma ya ce mata NADIRAH gatsau, abin nan yana bani dariya Aba, wai fa aunty kishi ne mai zafi ke fama da ita......" A hankali ya tsare Auta da kallo, har sai da ta fahinci kallon ya yi dan yawa ta dan TAKAITA tana kallonsa A nutse ya ce" Uman Aba, kina nufin ........., auta kina nufin wannan rigimar dan tana kishinaa ne?" Auta na murmushi ta gyada kanta, A hankali ya dan gyara zamansa yana dan cakude girairakinsa, kasa kasa ya ce" Ama, ana kishi idan ba'a son mutun?" Auta ta tsayar da dubanta a saman fuskarsa, sai kuma ta dan girgiza kanta ta ce" Abah, a sanina ba kishi idan ba so" Fuskarsa ne ya dora alamun dan damuwa, sai kuma ya koma ya zauna da kyau a ransa yana ayana' ni na san bata so na, ita dake nan tana jiran na bata takarda ta jewa Tuzurun kauye?, Ni din kuma ko ta yi yaya da nawa zuciyar.......?', sai kuma ya ringa nanata kalmar nashi zuciyan..................................... A hankali ya gyara zamansa da kyau yana sake dubam Auta, du a sonsa na ya zanta da ita sosai ko zai ji sanyi sanyi a zuciyarsa, domin dai shima da ya nemi wanda zai nufa dan sanar da damuwatsa ita kadai ya gani a idannuwansa Dan tabe baki ya yi yana girgiza kai ya ce" Uhum, Auta, wai yanzu HUZNAH ta gama mun fada, harda cewa bana sonta na fi son NADIRAH a kanta, kin ga hali irin na mata ko?" Da mamaki take kallon yayan nata bayan ta zuba masa dan cake din da suka yi, wanda NADIRAH ta shamaceta ta maka siga , ta ce" Abah, wani abu ya faru ne ama ko?" Dan dakatawa ya yi da abinda yake yi ya dana kalleta, sai kuma ya yi shiru bai bata amsar nan ba, dan gani yake yi maganar kamar ta fi karfinta , ko yace ba maganar da ya dace ya yi da ita bane Dan murmushi ta yi, zuciyarta na mintsininta da son sanar masa maganar cikin, tana cikin shakun idan ba cikin bane ba fa? Ama kuma irin yadda Inna ta fada da tabatarwa sai take jin kawai ta sanar masan "Dama maganin da take baki, kwaya ce ba asalin maganin samun lafiyarki bane?"..................... Ya fada da air na seriuss bayan ya ajiye plate din hannunsa bai dauki Cake din ba yana fuskantar Auta Gabanta sai da ya fadi, dan magana idan dai ta shafi Umma ko yayane daga mata hankali take yi Jiki ba karfi ta kalli Abahnta, sai kuma ta sake sada kai Ko yayane Abahnta ya gano wace Umma tunda har ya kawo wannan matakin a bincikensa Muryarta a raunane ta ce *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣4️⃣ Muryarta a raunane, kanta na kallon kasa sosai ta ce" Abah, sai bayan an mayar da ni gida, an sake dawo da ni na fahimci maganin ba na taimakona bane, na kwaya ne, daga baya ita da kanta ta sheda min hakan" Idannuwansa ya rintse, lokaci daya kuma ya bude a dan zafafe ya ce" Ta shaida maki haka? Kuma kika yi shiru baki ce min komai ba?, Bayanshi me da me take yi maki? Idan tana nuna maki soyayya a gabana du ba haka bane a bayan idannuwana ko?, A kan me zaki boye min? Me yasa?" Dan matsawa ta yi, dan irin yadda yake maganar a zafafe har ya fara dan daga murya, alamu na ransa a kololuwar bace yake ya bayana a tatare da shi Hankali tashe ta duka kasa kanta a kasa, hannayenta a jimke tana girgiza kai kuka na fitowa daga bakinta ta ce" Abah, ta yaya zan sanar maka cewa , Matar da Mahaifiyarmu ta yi mana nuni da mu kirayeta UMMA dan ta isa ba dan mun hada dangi da ita ba sai dan tsabar yarda da kaunar da take tsakaninta da mu baki daya cewa ta rikide ta koma aljana a gabana, tana zalintata , ta tsoratar da ni da kalamai masu muni a ranar da ta nuna min zata so aikata sabo mafi muni da ni, sabon da take aikatawa da wasu matan, na bijire na nuna ta rufa min asiri ko me take so na zama zan zama in dai zata rabani da wannan maganar, ta ju haushina a kan haka, ta kara kaimin yaki da ni da farin cikina, ta hanyar nunawa duniya mahaukaciya na zama sakamakon mutuwar mahaifana dan ina jahila wace bata da tawakali?, Take muzanta min ba dare ba rana , ta sakani zamtowa mahaukaciyar domin tsananin tsoronta da nake ji ya da ko maganarta aka dauko nake rikicewa, bayan ba za'a iya yin hira ba maganarta ba a cikin gidanmu, a cikin fada ana mutuntata dan ana mata kallon Uwa a garemu, a gabanka kana mutuntata dan kana yi mata kallon Uwa a wajenmu, Abah a yadda take da tasiri a rayuwarka ta yaya zan maka da maganar nan ka gane me nake nufi, bayan a cikin tsoratarwarta ta min nuni cewa idan har na yarda na sanar maka maganar nan ta yi alkawarin zata dora min shari mafi muni a rayuwa, sharin da kai da kanka zaka jefeni a matsayina na matar aure idan na aikata domin kana zartar da hukunci ne bisa koyarwar adinin musulunci, sannan ka dawo bakin ciki ya kasheka?, Wannan matar ce zan iya kokowa da ita Abahnah........." Da zafin rai, har hannayensa na bari ya katseta ta hanyar tafka mata tsawar da ta saka su dake ciki kamewa waje daya sunna kallon junna Muryarsa da fada fada ya ce" Kina nufin a cikin kazantaciyar rayuwar da take yi har ke ta so yi da ke? Kina nufin tsoratarwar da ta yi maki harda ta zata iya yi maki sharin Madigo?" Auta da ta hade kanta da gwuiwoyinta tana sheka kuka hankalinta tashe ta gaza furta koda A ne, domin zata iya rantsewa rabonta da ta ga bacin ransa haka tunda aka ce masa ta haukace, zai kwaso bacin ransa sosai ama fa zai yi kokarin boyewa a gabanta dan bata iya jurewa yanzu ne zata rikice masa da koke koke, sai gashi yau ya rikide mata tamkar ba shi ba , tamkar wanda zai iya zaneta idan ta yi wasa, sai hankalinta ya yi kololuwar tashi ta rasa yaya zata yi masa Zuciyarsa da ciwo, hankalinsa tashe, kirjinsa na tafarfasa yake kallonta, har Inna Hindu ta gaza jurewa dan ta gama fahimtar Auta kuma ta tsorata fa ba zata iya kare kanta ba, bayan yau din rana ce da ya dace ta kare kan nata, a dole ta fito da zumbulelen hijabinta har yana jan kasa domin Hijabin NADIRAH ne ta dauka dan a dakin Nadirar suke Tana zuwa jiki a sabule ta duka daf da Auta, hannayenta ta saka ta dago Auta ta rungumota jikinta , sannan ta sada kanta sosai, muryarta ba nauyi, a sanyaye sosai , kanta a kasa ta ce" Allah ya huci zuciyarka, ka yi hakuri ka yafe mata, ka gafarta mata ka yi mata uzuri, dole sai a hankali koda zata dawo yadfa kake so, ka tuna fa babu abinda ke saurin zama gaske irin yin abu da gangan, ko ciwo ka dorawa kanka da gangan yana iya rikide maka ya zama gaske, , Matar nan ta fi kowa kusanci da ita, rana tsaka ta wayi gari take haduwa da ainahin fuskarta, ta kuma fi kowa sannin ta inda zata biyo ta daureta gaba da baya, Auta kuma yarinya ce, a duniyarta kuwa ku hudu kawai ta sani, sai mijinta da yake bako a gareta, da wahala ta iya gane rayuwa ko ta gane cewar idan ta sanar maka kana da girma da hankalin da ba zaka tashi ka warware maganar kai tsaye ta yadda matar nan zata fahimta har ta yi mata sharin ba, ba zata iya gane cewar Allah ya azurtaka da ilimi irin na sarakuna, wanda yake banban da wasu kwakwaluwar, a dole idan abu ne aka fada maka zaka saurara ne na farko, zaka kuma yi duba irin naka ba wai na mai fadin ba, ka yafewa kanwarka domin a dole ta tsorata da makircin matar cen, idan kuwa ta kula ka jefe AUTA lalle kai kuma zuciyarka zata buga, kennan an bar talakawa a hannun su wa?, A irin wulakantar da Auta da ta yi sai da ta rabata da kowa, babu kawaye bale miji ko danginsa, uwa uba ta fitar da fuskarta a matsayin mahaukaciya, dan Allah ka fuskanci baiwar Allahn nan da ta zubar da komai ta hakura take yaki dan gannin ka take makiya, take kaiwa Allah kukanta ba dare ba rana har yanzu adu'arta ta karbu ta ga wannan ranar itama da ranta da lafiyarta, Ka yi hakuri dan Allah na shigo hurumin da ba nawa ba, ba dan na isa ba, ba kuma dab matsayina ya kai ba, ......ama Auta a nan muke zaune da ita, ta bude bakinta ta sanar min abubuwa da yawa wa'inda suka sakani kuka du irin kwamacala tamu ta kauye sai da lamarin rayuwarta ya gigitani...........idan a yau ka kasa fahimtarta ka karra rufeta ne a cikin hali na kaka naka yi, bayan kaine ABAHNTA......" Inna aka kare hawaye na bin kumata, sannan ta mike jiki ba karfi ta karra neman afuwarsa ta fice gaba daya a falon dan ji take yi idan ta zauna tana iya rushewa da kukan da za'a dawo bata hakurin itama, gwara ta he cen wajen bayi ta karra cakudewa da su ta yadda zata idasa nununa munafukan cikinsu wa y'arta saboda rayuwa ta yau da gobe da ta kama y'ar tata a gidan, dan kuwa babu gidan ubanda INDI zata je da cikin dan masu gida, ai it yanzu kuma tashin hankali ya kau, Auntynta da rai tana hannu mai kyau, sai shagali yanzu zata sake fuskantar karamar arniyar cen Sosai jikinsa ya karra yin sanyi, hankalinsa kuma ya karra tashi A birkice ya dawo kasa inda Auta ke dukunkunne bata daina kukanta ba, haka da Inna zata fita yana gannin yadda ta yi kamar zata bita, kennan tsoronsa ta ji da ya yi mata ihu? Shi kuwa ya yi ne a rashin control din kansa, a ganninsa ta yi wasa da shi ta yadda take tunanin zata kawo magana mai girma irin wannan ya wani banzatar da ita ta zauna shekara da shekaru tana shan wahalar arniya banza da wofi! A hankali ya dagota ya matsota gefensa kamar yadda yake yi mata a dama idan tana hali na rikicewa, A sanyaye yake taping din bayanta yana dan riko hannunta dake jimke a cikin nasa Muryarsa a raunane, hankalinsa du a tashe ya ce" Ki yi shiru haka Uman Abahnmu, haba Mariya mai baban daki, haba matar Lamido , dubi nan, dubi ban fa yi fushi ba dan wanu abu sai dan jin ciwo a zuciyata, Auta ina gefenki, ina tare da ke ba dare ba rana ina fita da isa da takama na je garin wanda na ga dama na kwato yancin wanda aka cutar na dawo kasata na kuma ja layi na tsaya na zartar da hukunci a zauna lafiya ama na gaza gannin hali na ukuba da aka saka min kanwata?...........kin san me haka ke nufi a wajena?, Auta na yi karatun rayuwa tunda na hau karagar mulki, abinda yake karkashin tunanina ni da kaina na san wani lamari ne na ubangiji, mutun kuwa na yi masa karatun da yake da nisan gaske, na riga na san cewa babu abinda ke gagawar juyar da kwakwaluwar dan Adam irin abu ukun nan *ARZIKI, MULKI, MACE*, a kansu dan Adam na iya mance kansa da asalinsa, a kan neman duniya da abinda yake cikinta dan Adam na iya mantawa ba matabaciya bace ya saki jiki ya yi ta tafka lamuransa sai a cikin bulala ukun nan daya ta riske shi sai kuma a dawo ana dana sani ko a rikice a bar dabi'u na alkhairi a koma kwashe kwashe watau *RASHIN LAFIYA, TSUFA, MUTUWA*, wa'inda basa yiwa kowa uzuri ko su baka dana ka sake gwada wani tashin daban da wanda ka yi..................................." Ya ajiye maganar yana jan numfashi, dan ya zame masa jiki idan dai ya yi doguwar magana irin haka yakan ji ya gaji ne tikis kamar wanda ya yi wani aiki , sai yana yi yana ajiyewa ko zai iya karasa yawan maganar A hankali ya sake budar bakinsa ya ce" Tabas mun bata yarda, ta ci amana, a lamarinta yanzu abu daya ne ke cikin duhu a zuciyata shine rasuwar mahaifiyata, me ya hadasa kumburin cikin ANNA kai tsaye? Harta a likafaninta cikinta a tashe yake sosai wanda na jima a cikin tunanin nan, da kuma bakin jinnin da ya fita ta hancinta..............Shin matar nan ta kai wajen da ta kashe min uwata Auta?" Dummmm gaban Auta ya yanke ya fadi, zuciyarta ta shiga yi mata zafi domin tunano kamawar da ta yiwa Umma da irin rikicewar da ta yi kafin kuma ta ga ta sauke ajiyar zuciya a lokacin da ta ji jan numfashin Mai dakin Mai martaba na karshe, jan numfashi da ya yi wani irin tsayi ya fita bai kuma dawowa ba, kukansa a kunnenta da irin ajiyar zuciyar da ta ga UMMA ta sauke alamu na kwonciyar hankali ya wadata fuskarta, ama kuma sai ta kamata ta kaita dakinta ta rufo ta fada mata mamanta ta mutu , bayan tana cikin kukan wai mahaifinta ya rasu.............ta barota a ciki, ita daya kwal da ranta , ta yi kuka har nunfashi ya yiwa kofar hancinta kadan ta summe, wanda sai a washe gari aka ringa nemanta hankalin ASADEEK din a tashe kamar zai summa dan tashin hankali da kyar aka ganota a dakin nata summe....... A harhade ta sanar masa komai , dukkan abinda ta sani, irin abinda ta gani a fuskar UMMAN har rufewar da akai mata Umma ce ta rufeta a daki Ya jima idannuwansa lumshe, gaba daya ji yake yi me kuma ya rage masa na jin dadi a duniyar nan? Gaba daya ji yake yi sarauta bata yi masa rana ba , ji yake yi da ace su ba kowa bane da ba'a rabe su dan a cutar da su ba, saima yake ta kokonton anya zai iya sake yarda wani ya masa shigar da Umma ta yi masa a zuciya ta cutar? Wani tarin takaici gefe daya kuma yake mintsininsa, wannan maganar idan har haka ce dole zai ji ciwo a zuciyarsa mai tsanani, domin ya so ne ta rayu a cikin gidan kaso ta yadda zata yi doguwar rayuwa tana kallon abinda zai yi ta nukurkusarta, idan kuwa harda maganar kisa a ciki ai dole za'a kasheta itama, sai dai kashetan nan walahi walahi ba zai aikata da wuri ba, bi'izinillah sai ta yi rayuwar gidan kaso koda ta shekara biyu ne tare da fargabar yau ko gobe, da rikicin tunanin kwonciyar kabari da irin abinda ta aikata, sai ya sakata daki mafi muni da duhu ta yadda zata ringa auna a duniyar kennan ina ga lahira da nauyi irin nata? Sai ya wakilta malamai irin masu zafin wa'azin nan sun ringa zuwa du safiya ta Allah sun yi wa'azi a kan mutuwa da girman laifin wanda ya cutar da bawan Allah da irin azabar dake cikin wuta, uwa uba hanyoyin da za'a tarar kafin a kai tsayuwar hisabin, bi izinillah sai ya bata damar dandanar ukubarta daidai misali, ta yadda zata zamo mahaukaciya ta gasken gaske ba wai ta karya da hade haden magani ba, sannan zai zartar mata da hukuncinta ta hanyar bawa du mai iya ganni damar zuwa dan hakan ya zamo babar bulala wa mai rabon dacewa da shiriya tun kafin lokaci ya kure masa Daga hakanan kuma ya kasa furta komai sai idannuwansa da yake kawarwa baya so Auta ta kalla du irin yadda take son kallon dan kamalta abin a zuciyarta ta san yana cikin wani hali mai wutar fasara, "ABAH" Auta ta fada a sanyaye tana kallonsa Da kyar ya iya daga idannuwan nasa yana kallonta Auta ta lumshe idannuwanta cike da jin tausayinsa a zuciyarta, ita ta fi tausaya masa fiye da nata, dan shi ya zame masa dole ya dauka ya kuma shanye, ya dauki damuwarsa ya kuma dauki ta talakawansa Murmushi ta dora a saman lebenta, a hankali ta ce" Abahna, Aunty NADIRAH....... Au, Momy NADIRAH fa tana da ciki, Abahna zamu samu baby muma ABAHNA....." Ta karashe tana kallon yannayinsa a lokacin da ya zarro manyan idannuwansa yana kallonta, kamarma bai yarda ba, kamar kuma abu ya shigo maka kai tsaye, dama burinta kennan abin ya shigo masa kai tsaye , cikin tarin duhun da yake gani haske ya ratso alfarmar annabi da Alkur'ani............. Muryarsa a cen ciki ya iya sake budar bakinsa da kyar yana kallonta idannuwansa a wajen nan ya ce" Me kika ce?" Auta ta sake maimaitawa, yanzun har yar dariya take yi tana share hawayenta hadi da jan hanci Jikinsa ba karfi , ama kuma yannayinsa na cenza salo ya dan rangwabar da kansa aa sanyaye ya ce" kuma tsokanar da zaki yi min kennan Auta?............" Daria Auta ta saka mai dan sauti kadan, ta ce" Hello people, morning all *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣5️⃣ Ina kuke MATA, MATA masu ji da kansu,MATA masu aji, WA'INDA suka san girma da darajar gyara, WA'INDA suke iya cire kudade masu yawa dan gyaran kansu? Ku garzayo ku tuntubemu, ama ku tabatar jakarku ta cika taf, domin bamu da lalan kaya bamu da na kudi kadan, kayanmu gyara ne hajia magani ne na mata mai mayar da busashe tamkar teku..........ku tumtubemu ta wannan numbar *80229915* MAIMUNA MATAR ABDULAHI..... Sai kun zo Daria Auta ta saka mai dan sauti tana kallon irin yadda yayanta ya yi kamar wani bakin marayan dake jin yinwa ta ce" Abah, ana wasa da irin maganar nan mai daraja da girma?, Ama fa ba likita ne ya fada mana ba, Mamah ce ta sanar mana, Aba ka san datijai sunna ganewa ko yau ka tashi da ciki sunna iya fahimta , a shekaran jiya n....................................................." Sauran maganar ne ta hadiye tana zarro ido hadi da binsa da kallo, domin kafin kace meye wannan ya mike daga zaunen da yake ya durfafi dakin da Nadirah ke ciki Bai tsaya tsaye tsaye ko jin kunya ba ya kama ya bude ya shige cikin dakin, hakan ya saka Auta sakin murmushi ta mike ta fice da wayar wajen Inna HINDU ta janyo kofar ta rufe da ky ta shiga tafiya a nutse da wayar tana neman layin wanda take mararin jin muryar mai shi _________________________________ Karar bude kofar ta ji, tana tsaye gaban madubi daure da tawul, wanka take shirye shiryen shiga dan kuwa tun na asuba da ta yi kafin ta daura alwallah dan jikinta ya saku sai yanzu da zata yi wani, tana kallon mamanta da ya kumburo, bama irin kansa da ya yi mata wani iri ta yi saurin daura tawul din tana hade goshi a zuciyarta tana ta tunanin shin zata sanarwa Innarta abinda nononta yake yi ko zata yi shiru da bakinta ne? Idannuwanta suka sauka a saman fuskarsa Irin kallon da yake binta da shi ko makauniya ce ita dole zai samu effet a jikinta Da sauri ta dauke idannuwanta ta juya ta shiga rarumar abinda zata rufe jikinta gaba daya , kaffafuwanta da hannayenya sai bari suke tamkar mazari A hankali ya sake lumshe idannuwansa ya ciro bayansa daga jikin garun da ya jingina ya ringa takowa zuciyarsa na bugawa har ya karaso inda take tsaye jikinta na mugun rawa ya rungumeta ta baya a hankali ya dora kansa a saman wuyanta lokaci daya kuma ya kama hannayenta da nasa, yana sake lumshe idannuwansa yana fitar da huci daga zuciyarsa ta bakinsa mai dumi a dokin wuyanta, muryarsa a sanyaye ainun, sannan a cen ciki ciki ya ce" Dan Allah, ki sasauta min haka mana Tarhanine…......" A hankali ta ringa daidaita kokowar da take ta son yi da shi, zuciyarta na dokawa da masifar karfi, kanshin jikinsa na ratsa dukkan wata kofa ta hancinta, bakinta, kofofin jikinta sunna wanzar mata da muguwar kasala da mutuwar jiki ta karra lumshe idannuwanta tana cije jinjirin lebenta tana jin zafafar zufa mmai dumi na sauka daga gaban goshinta tana zuwa jikinta A sanyaye, muryarsa na matukar son halakata ya sake riketa a jikinsa a hankali ya ci gaba da fadin" ki tausaya min haka dan ALLAH, kin ga ni marayaa ne gaba da baya, wace ta rikeni ta wulakantani......, Kin san a yau ji nake kamar zan mutu?, Zuciyata ciwo take min Indinah...., Zafi nake ji sosai momyn Autah.........." Ya karashe yana sake riketa a kirjinsa A hankali ta ringa son juyowa har ya fahimta daga riketan da ya yi ya dan sasauta mata ta yadda ta juyo idannuwanta lumshe sunna zubar da ruwan da baya san ko na meye ba Kanta ta dora a saman kirjinsa ta danna da dab karfi tana jin irin yadda kirjinta ke bugawa, ta rasa a wani mataki zata ajiye abinda ke son girmamar tunaninta Muryarta a raunane ainun, cen cikin da bata yi tunanin zai iya jiyota ba, bayan ta dora kaffafuwanta a saman nasa hankali kwonce, muryar cen ciki ta ce" Aban Datawa, kai kuwa mai zai raunana maka zuciya har ya saka ka bugun zuciya haka?" Subahanalah, watau ko a ina tuzuruwar kauye ta koyo salon nan ta koyo shi daidai da zamani, idan da gangan ta yi zai iya cewa Allah ya karro rashin ji, idan kuwa a rashin sani ta yi haka take tabara a jinnin jikinta ne zai iya cewa Allah ya karawa mata daraja duniya da kiyama , Sai ya ringa jin kamar ya fashe mata da kuka wollah, kamar itace babar shine karamin, bale da ta zagaya hannunta daya ta rungume bayansa da shi, sai ya ji shi a yau baya jin wani dar a kan tuzuruwar kauye A sanyaye ya furta" Waye ni, da ba zan ji tsoro da abinda zai iya mugun tsoratar da ni bs?" "Kaine fa , UMUGHLUK ITIBEL, kaine jiran Maza, kaine Aban su Innata........" Ta fada a sanyaye bayan ta dago rinanun idannuwanta tana kallonsa Hawayen dake saman kumatunta yake ta kallo, a hankali ya ce" Nine kuma bakon INDIH, nine wanda indi ta ki duba, nine mai bara da kokona a gabaan Indi, NADIRAH zuciyana na dokawa ne idan na kalle ki na shiga halin tsaka mai wuya a tunanin kar aje har yanzu kina kwana da wanina a zuciyarki............" Ya karashe yana fadin wani da wani yannayi na jin daci, wanda kiri kiri ta fahimci hakan Idannuwanta ta mayar ta lumshe, a ranta ta shiga ayanno kalmar wani, da kuma wannan dake gabanta, A dama fa, tunda ta ga ASADEEK ba rawani, sai da ta ce dole zata kiyaye yawan matse masa waje da kallo dan kar Aminu ya dawo yi nata muni a idannuwanta, sai kawai Aban datawa ya tube a gabanta malan...., Ba fa zata manta ranar da aka yi tsere a kauye ba, samarin kauye suka cire rigunnansu dan a yi gudu a sake jama'a, kowace budurwa ta je gaba tana doka yar gangarta dan ta karrawa gwarzonta kwarin gwuiwa, ana sako samarin nan suka bazo a waje jama'a yar dubu ta karewa Aminu kallo tace Ke indi duba ku ga Aminu kamar dan yayen kaka, tana kallon Aminu ta hango wuyan da kan sunna rangaji na gudu, dan cikin nan nasa ya yi dan tumbin kunnu gefe daya, Aminu gudu yake kansa da kafarsa yana jan wandonsa, a dole ta kawar da kai domin har ga Allah yar dubu ta cuceta, ta jims tana nazarin zululu wuya uwa marikin lemar da ta ringa hangowa, a dole da Kato ya cire riga ta baza ido tana kallon ikon Allah, Aban datawa kam ba dai kirji ba, harda wasu gida gida a cikinsa, ko baua shan koko ne shi? Hannunsa dake ta yawo a saman cikinta, irin shafawar da yake yi da son cusawa samn cikinta ya sakata tuna abinda aka ce, wai tana da ciki, sai ta karra jin wata kunya na son lulubeta wollah, idan labari ya fita cewar ta samu abin nan da sai an yi abin nan ake samu yaya zata kalli jama'a, jama'a su kalleta? A hankali take dan ture hannun nasa, hakan ya saka shi sakw tsureta da kallo zuciyarsa na dan bugawa a hankali Muryarsa a sanyaye ya ce" Ba dai zaki daina tureni ba ko?, Wai meye tuzurun kauyen ya fi ni da shi?" Kai jama'a, sai da ta zabura, Aminun ne tuzuru? Wannan ai kalmar aban birni ce, ba shiri murmushi ya subuce a saman fuskarta, ta sada kanta kasa kasa ta ce" Ka takurawa tuzurun kauye , bayan kaima mijin HUZNAH ne" Murmushin ne shima ya sake kwonciya a saman fuskarsa, ya salam, da gaske kennan itama tana jin haushin matarsa dan tana kishinta, wannan dadi da yaya zai kamanta shi? Jinsa yake a cikin zuciyarsa har cen kasa kasa Gabansa na dari dari ya fitar da abinda ya fi saka shi bugawar zuciya, a sanyaye ya ce" Wai kina da ciki?" Dum ta ji gabanta ya fadi, da sauri ta rufe idannuwanta tana son janye jikinta daga nasa da kuma harhade fuskarta hankalinta na dan nuna alamun tashi Sakinta ya yi ya zuba mata ido yana kallonta har ta karasa wajen gadon ta zauna ya saka Hannayenta ta dafe kanta da su tana kallon kasa Sosai hankalinsa ya nemi tashi, Juyawa ya yi yana dafe gaban goshinsa dan kansa ne ya sara masa Lokaci daya ya yankewa réaction dinta hukuncin hakan na nufin bata son cikinsa ne?, Cikin da ya tabata kowa yake jira? Cikin da za'a fitar da maganarsa yau garin AGADAZ da kewaye sai an wuni ana bikin samunsa? Cikin da kowace mace marar aure wace take cikin hurumin malakarsa zata so ace a cikinta ya samu? Hankalinsa a matukar tashe ya karaso gabanta, yana tsayen nan , muryarsa a tausashe ainun ya ce" Zaki mike, mu tafi wajen likita ya aunaa ki, idan kina fauke da cikina daga bakin wannan lokacin zaki dawo rayuwa daf da ni, ba zan iya raba daki da ke ba sai idan ranar yar uwarki ne, a bangarena inada dakunna sun ishemu daga ke da ita da ni kowa ya kama dakinsa,......." Gaban goshinsa ya karra rikewa dan gaba daya abin ke son saka shi fasa mata ihu bayan bai sani ba idan har cikin ne da ita ko ana yiwa masu ciki ihu A hankali ya ce" Ban saba da irin wannan shara'ar ba, kin ga abin ya shafi cikin zuciyata ne, NADIRAH da garaje kika shigoni kika gama shuke shuken ki, ban hannaki ban ruwa a jikina ba, a yanzu kuma ba zan hannaki cire itatuwanki ba, sai dai ni din gonar ki ne, baki da wata sama da ni, ke din kuwa kasar cikin gonata ne,..... Ba zan iya hakura da ke ba, ba zan iya barawa wani ba, ba kuma zan yarda ki min wasa da cikina ba!.............. Sai dai Allah ya baki hakuri................., Ba zaki bata min cikina ba, ba.................." "Batawa?, Wani irin batawa?" NADIRAH ta fafa a sanyaye, tana kallonsa, irin yadda jijiyoyin jikinsa suka mike yake zuba masifa har yana hade kalma da kalma ta rasa me aka yi, me ya kawo haka, me yake nufi Dakatarwa ya yi, ya hadiye magangannunsa gaba daya yana kallonta, har sai da ta sake maimaita tambayarta, sannan ya shiga tambayar kansa shima dan son sannin me yake nufi Zaunawa ya yi a gefen gadon yana hade hannayensa a saman jikinsa , tamkar ba ASADEEK namu mai tsayawa a gaban duban al'uma ya kirta doka a bi ba, yana kallonta ya ce" Wannan hade ran da kika yi ba tsare tsaren gudun min bane kike dan na miki ciki?" Da sauri ta rufe fuskarta da hannayenta , ka ji fa danyar magana daga bakin Aban datawa A hankali ta kuma bude da dan mamakin dake saman fuskarta, a hankali ta ce" SAI KACE SHEGE?" Maganar, ta zo masa a ba zata, hakan ya sa ya dan saki bakinsa kadan yana kallonta Nadirah, ta sauke ajiyar zuciya tana dan kawar da kanta, kasa kasa ta ce" To ko shege ne tunda ya samu ai bana tunanin akoy dan Adam din da zai sakani zubarwa, bale dan halal....., Kawai dai ni mamakin da nake sau nawama aka yi abin nan, kuma innata bata san abin nan ya samu ba, idan aka ji ai na shiga uku, bama a kauyen labba, Aban Auta mune fa ke zuwa gidajen amare a LABBA idan muka ji labarin cewa wata ta dauko ciki daga kaita mu titsiye yarinya sai ta fara kuka a biyomu da gudu, Aban datawa a kai kashe wajen kakar yar dubu, dan ni basa kaiwa Innata kashedi, yau idan ya faru da ni kaf kauyen Labba sai sun sakani a dandali" Murmushi yake yi, kumatunsa sunna lotsawa, hakoransa a fili, Rayuwar kauye na son saka shi a baban nishadin da baya tsinta a rayuwar Birni, furucinta ya saka masa jin wata saukar nutsuwa a cikin zuciyarsa......., Kennan ba zata aikata sabo ba dan dan Adam ko dan zuciyarta, dama ta matukar bashi mamaki da ta ki amsar tayin kashe shi bayan ya shigo rayuwarta a matsayin wanda ya katse mata soyayarta da wanda take so tun yarinta, sai kuma yanzu ......idan har tana da cikinsa zata rainar masa abinsa ne?, Ya kasa gaskata irin dokawar da zuciyarsa ke yi da karfin gaske har sai da ya wartota jikinsa ya rukunkumeta irin rikon da zai iya rantsewa bai taba yiwa wata mace a duniya ba sai gawar mahaifiyarsa a lokacin da ya samu a shinfide babu numfashi Idannuwansa rufe yake kaiwa dukkan wajen da ya samu sumba, har ya samu ya hade bakinsa da nata a hankali ya ringa tsotsa..........idannuwansa a lumshe yana kokarin lalubarta, har ya ji hannunta saman nasa ta rike a hankali ta kai cen wajen mamanta dake ta yi mata zogi ta dora, idannuwanta a rufen nan da mugun jin filing muryarta a raunane ta dan cire bakinta a nasa tana boye fuskarta ta ce" Nan ne, ke damuwa, yana ta so ka yi irin abin nan da kake yi Aban datawa......" A dole Aban datawa ya manta dukkan wata damuwa da ta saka masa nauyin numfashi, ya kuma manta a ina ya tardo yar mutane ta hanyar janye wannan abu da ta daura a kirji ya yar idannuwansa na sake kankancewa yana neman kurma ihun MAZA ya damketa, ba ju ba gani ya ringa juyata kamar yadda yake juya akalar dokinsa idan ya hau, ya kuma sameta da wata irin biyaya domin du irin yadda ya yi tunanin zata gajiya da wuri sai ta bashi mamaki ta hanyar nuna masa ta fa shigo gari ta kuma harbun dan kuwa sai da ya darji mata iya darza ya kuma san ya zowa mata sun amshe shi................... Ba shi ya tuna a inda suka yayada manufarsu ba sai da suka fito daga wanka, a lokacin ne itama ta ringa tambayar a ina ya bar Auta fa innarta kafin ya shigo? Kiri kiri ta nuna wannan din ai laifinsa ne ya zo mata daki Fisabililahi ya sakata aikata kayan kunya Shi dai murmushi yake yi yana binta da kallo har ta gama shiryawa, yana tsaye yana kallo ta saka zumbulelen bakin hijab ta dauko nikaf dinta da safa bakake tana fadin" Wai Aban Auta, dolene mu je asibitin? Idan mun je ai ba za'a min allura ba ko?" Kai ya girgiza da sauri, a tausashe ya saka hannunsa cikin nata kasa kasa ya ce" Babu mai yi maki allura, zamu je ne a tabatar mana, kuma ba asibiti zamu tafi ba, gidan SHEIK ne zamu je, kin ga ni ba zan je asibiti haka rana tsaka ba ko?" Murmushi ta yi ta saka safar sai tafukan hannayenta a waje, a hankali suka fice tanaa sando shi kuma yana murmushi yana biye da ita ta biyayiyar hanya suka bar bangaren nata suka wuce nasa A cenma zama ta yi a falo shi kuma ya haye sama Yana zuwa suturarsa ya cenza zuwa sasauka, ya yane kansa da sasaukan rawani ba asalin wanda za'a iya gane shi ba, domin du buzun mutun dai an sanshi da rawani ba sai sarki ba, ya saka takalmansa masu saukin tafiya Yana fesa turare yana ta doka murmushi kira ya shigo wayarsa Da dan mamaki yake kallon numbar, domun numbar mahaifin HUZNAH ne, sarki Muhammad, bai taba yin kiransa ba kai tsaye, hakan ya saka shi komawa ya karo dakin da kyau, ba dan komai ba sai dan baya so yana magana da shi wani abu ya katse, haka kuma ba zai so ace NADIRAH ta san cewa HUZNAH da SHI babu mu'amala irin ta aurataya a tsakaninsu, zai so ace dukkan abinda yake sirri na daya a wajenshi ya zauna a wajenshi kadai, ba dan komai ba sai dan gudun matsaloli irin na yau da kulum na mata, ba zai taba bude sirrin daya a gaban daya ba, koda ta ji to ta je ta karata da wasi wasi ba zai bata fuskar ta yi masa tambayar idan haka ne ko ba haka ba, hasalima ba huruminta bane hakkan, gaba dayansu zai yi masu wannan adalcin dan gannin ya kaucewa cece kuce da matsaloli na yau da kullum A nutse ya amsa salamar da Sarki ya yi masa da girmamawa, sannan ya sake mayar masa da gaisuwar da ya yi masa dan bashi girmansa A tausashe sarki MUHAMMAD mai adalci ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣6️⃣ A tausashe sarki Muhammad ya ce" Allah ya karra maka lafiya, da nisan kwana, ya sa a gama da rikicin mulki lafiya, ina fatan ba'a fada ? Na yi kira a irin wannan lokacin ina fatan ba'a cikin wani uzuri mai karfi?" Dan murmushi ya yi, a duniya yana girmama datijin nan sosai, domin mutun ne mai daraja, masarautarsa ba babar masarauta bace, asalima kauye ne a da a hankali ya zama kauye ama mai shige da gari dan yana tafe da jagorancin sarakunna masu talafawa talakawa da kawo ci gaba a garinsu, Tunda ya auri yarsa ba zai ce ga ranar da wani abu na batanci ya shiga tsakaninsu ba, haka kuma tunda girma ya same shi na jagorancin al'uma bai taba kama garinsa da laifi mai girma ba ko karami, ya iya da rikicin garinsa yana kuma kare girmansa, bai saka kwadayi a gabansa ba bale halaya na rashin da'a su aure shi, sosai ake girmama shi a layin datawan sarakunna masu mutunci, haka a tsakaninsu na sarakunta zai iya cewa Alhamdulilah A tausashe ya ce" Babu takura, ranka shi dade, Allah ya karra kusanci da fiyayen halita Sallallahu alaihi Wa salam" Da amen ya amsa cike da girmama ASADEEK, domin kiran nan da ya yi masa sai da ya kori kowa shima ya samu nutsuwa dan su zanta Cike da jin nauyin maganar, da kuma kunyar abin dan bai taba fuskantar irin haka ba ya ce" Rikici ne na Mata Allah ya karra maka lafiya, koke koke da magangannu masu rikitarwa sun same mu da sanyin safiya daga mai dakinka, harda neman alfarmar a nema mata alfarmar ta zo gida a nema mata magani,.........shine na dakawa abin tsawa cewar ba dai gidana ba, sai daga baya nake ta tunani a kan lamarin, magangannunta du a sasabe ta banu shi, ta kuma ce ta gaza gane inda ka dosa.....ta yiwu bata sada kai ba bale ta fahimtan, dalilin wannan ya saka na yi kira, ba dan komai ba sai dan na fahimci shin wani hali ta dauko na rashin da'a wanda ya cencenci na kawota na yi mata bulala, ko kuwa mun yi wasa an cin matan da gaske?" Cike da jin kunyar Sirikin nasa ya ce" Alhamdulilah, a zamana da ita zan iya cewa dukkan namijin da ya dace da uwar gida irinta zai rayu cikin salama, babu abinda ta aikata da zata fuskanci duka ko tsawa, ina fata ta gama rayuwarta a karkashin innuwar aurena na birneta ko ta birneni cikin aminci da salama.......," Ya dan sasauta, domin magana ce yake yi tsakaninsa da wani sarki, koda sirikinsa ne ba matansa bane, kai zai iya cewa yana zama suda sarkin zance ne idan yana gaban yan matan nan biyu da suke gannin maza a yadda suke, bama irin tuzuruwar kauye, takan shanye masa man kansa tasssss abinta A hankali ya dora daa fadin" Akoyma maganar rashin fahimtar, domin na yi mata tambayoyi dan mu samu matsaya sannan mu san ta inda zamu hau binciken, idan baka manta ba ka yi kirana a jiya kana yi min jajen batan bafana kuma mahaifin iyalina na sanar maka yana hannuna harma nake sheda maka ba shine mahaifin NADIRAH ba na fayace maka abinda aka aikata min har ka samu bacin rai da rikicewar tunani ?, To a yanzu zan sanar maka ina kyautata zaton a zuwanta amarci tun kafin a fahimci lalurar dake tare da mu an hadata da ciwon a jikinta............, Dan kawai na dan kwatanta mata ciwon a tare da ita ne yake ba a tare da ni ba, dan mu samu mafita mu nemi magani ne ta dan rikice...........a wannan fannin takan rikice dama, sai a hankali kuma ta gane........................" Da mamaki, muryarsa da alamun bacin rai ya ce" Subahanalah, Kana nufin lalurar nan dama a tare da ita take?" ASADEEK ya dan yi jimmm, kafin ya bashi amsa a nutse yana dab kawar da dubansa tamkar a gabansa sarki Muhammad yake Sarki Mohammed ya ce" Ka ji rashin hankali, aiki irin na wanda bashi da tunani!, Ita fa HUZNAH dama mahaifiyarta kan cewa sai an yi mata nema irin na kishi, domin tana da wannan matsalar sosai har aan sani, in ba rashin hankali ba abin nan da yake jikinki, namijin bai fito maki da rashin da'a ba ke zaki yi masa rashin wayo?, Ko a ina ta hafu da ciwon sunnan ciwon a jikinta ba a jikinka ba, takan mance kai sarki ne ko wani lokaci aurwn wata na iya kamaka ? Ko a rashin adalcinta da son kanta so take a tsaya iya ita kuma jiki da jinni? Sam bata yi aiki da ilimi ba, ta kuma so kanta da yawa, ka yi hakuri da hali na shirme da shashanci irin na wasu matan, manyanma wani lokacin idan suka tafka maka wani abin sai ka samu kanka da jin juwa,sai hakuri ana tafe ana taro su ne su, in sha Allah zan taso jakadiya da dan taimako dan a talafa maka, a irin wannan halin da kake ciki idan bata yi hankalin kwontar maka da hankali ba ai bata isa ta tayar maka ba, ka yi hakuri, ko aikin waye in sha Allah zai karye, domin mun sha haduwa da irin haka a kauyen nan, ka san mutane akoy son kai" Dan murmushi ya yi shi dai bai ce komai ba har Sarki ya gama fadansa, ya kuma tabata HUZNAH ta cira bata nuna ba dan abanta bashi da sauki a kan lamarinsu, sannan ya tabata za'a sama mata maganin bi izinillah................. Sun karra tataunawa a kan damuwar dake gabansa, dan kuwa yakan sanar masa wasu sirikansa sannan suka yi salama ya mike ya fice da wayar a aljihunsa ya sauko yana adu'ar Allah ya sa bata yi tafiyarta ba Rarashi ya yi kafin take yarda ta mike su fice bayan Sarkin yanka ya shaida masa sunna iya fitowa gidan ya dinke da jama'a ana cakude ba lalle bane a gane fitowarsa daga bangarensa A hankali suke tafe har kusan motarsa dake bangaren nasa Da kansa ya zagaya wajen da zata shiga ya bude mata yana kallon idannuwanta dake cike da ruwan rigima yana murmushi har ta zauna ya dan gyara mata abin rigarta sannan ya zagaya ya shiga inda direbansa ya bude cike da mamaki da kuma kamewa gannin UMUGHLUK ITIBEL ya budewa mace mota ta shiga Yana zama a hankali ya janyota jikinsa ya rungumeta a kirjinsa, motar ta daga ta shiga tafiya yana bin masarautar da kallo, tarin jama'ar dake kai kawo , kowa da shagulgullan dake gabansa, ama bangarensa daidaiku ne dake son ganninsa manyan mutane sunna jira har ya tashi daga barci cewar masu tsaron kofarsa Ajiyar zuciya ya sauke..........., Kasa kasa ya ce" Barci kike ji?" NADIRAH ta dago ta dan dubi idannuwansa dake zagaye cikin rawani Kasa kasa ta ce" Kan ne ke karra min zogin, ko na bude maka?"....... Ido ya rintse da karfi yana riketa a jikinsa, zuciyarsa na dokawa A hankali ya ce" Idan kika yi hakurima kadan ya rage ki halakani Indi.....ba sai kin bi ta haka ba........" Kallonsa take baki cune tana dake bararajewa a jikinsa Ai tunda ya yarda ta gane menene shi kuma lagonsa ba zata taba yi masa da sauki ba, bata san dalili ba, kudirinta na aikin dan lokaci ke rikidewa a cen kasan zuciyarta yana ayanna mata kalmomi kamar haka' ki fa yi da gaske, kar kishiyarki ta kwace zuciyar mijinki, kema macece ce, koda baki je boko ba ba yana nufin MAHAUKACIYA kike ba, babu kuma litafin da ya fi na addinin musulunci, tunda adini ya nuna hakan din baban lada ne ita kuma meye zai tsayar da ita? Saima ta fara gabatarwa Aban datawa rawar da ta tanadarwa wancen macucin da ya yiwa mata biyu ciki! A hankali ya daan bude lumsasun idannuwansa, har sun kade sun yi ja da wasu yan ruwa ruwa kadan a cikinsu sun kuma shanye Hannunsa ya mika kadan ya dan saki labulen dake tsakaninsa da direban da kuma dogarin Fada a hankali ya janye rawanin fuskarsa ya sake talabots ya nufo fuskarta idannuwansa na sake neman rinewa A hankali ta tare shi da hannunta tanna dan zarro manyan idannuwanta kasa kasa ta ce" Abam datawa me zaka yi?" Kasa kasan shima ya ce" Daneki zan yi Uman datawa" Kunya kuma sai ta dirar mata hadi da yar dariya, a hankali ta ce" A mota fa muke ka manta ne?" Kasa cewa komai ya yi sai kallonta yake yi A hankali ta sake cewa" Kai kuma baka iya abu a hankali ba ka sani sarai ko........., Ni dai da shi din kadai ka yiwa yadda kake yi masa da ka taimakeni, kaikayi yake yi ya kumburoooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooooo" Subahanalah, lalle idan su Umma basu kashe shi tuzuruwar kauye bata zo da wasa rayuwarsa ba Shin bata san bakon abin yake ba, abin na girgizashi komai kankantarsa? So take yi ta idasa shi da dan kuzarinsa Maganama ya kasa yi, a dole ya mayar da idannuwansa ya rintse ruf ya kuma jinginar da hannunsa da gefen kofar ya jimke shi ya dangale habarsa da shi, ba komai yake karra haskowa a irin wannan lokacin ba jama'a sai tuzuruwar kauye a mikowar ingoma.....kai Allah dai ya yiwa mata albarka Har suka isa yana a wannan yannayi, ga idannuwa sun masa wani iri ga maza sun mumurde kamar baa yanzu aka sauke su ba Bayan sun tsaya a baban filin gidan SHEIK direbansa da dogari suka fice suka fita waje suka hade da Sarkin yanka dake tsaye yana kai kawo , shi kuma da kyar ya iya sanarwa Sheikh cewar sun karaso Ba'a dauki wani lokaci ba sai ga Sheikh ya dosa motar da matarsa wace yau itace da aiki, watau Likita yana gaba tana biye da shi cikin shiga ta musulunci tana dan murmushi ta tsaya daga nesa kadan kanta a kasa shi kuma ya dan karaso ya bubuga motar yana tsaye da tunanin ko basa cikin motar ne? A sanyyaye ya ce" Ki daga ni, kin ji INDIH?" Murmushi ta yi a boye ta daga shi tana gyara jikinta, a sace ta kalli nasa jikin, sarai ta fahimci ta fa motsa maza hakan ya sakata sake yin boyayen murmushi ta sada kanta ta ki motsawa Kasa kasa ya ce" ALLAH ya shirye ki " domin sarai ya san har da gayya ta aikata masa aiki, ama ba komai ai daga hau har gobe tana matsayin mai gadonsa, zata gane maza fa mazan ne Allah kuwa Sai da ya gyara sosai sannan ya bude ya ziro kafarsa yana kakawar da idannuwansa dan kar su yi ido hudu da SHEIK, domin ya ga sai son sai ya kalle shi yake yi Fitowa ya yi ya rufe sannan ya zagaya yana ji matar SHEIK na miko masa gaisuwa ama bai iya amsawa ba sai da ya karasa ya bude motar nan hankali kwonce ya mika mata hannu, ta dora nata ya taimaka mata ta fito yanzuma ya karra gyara mata abayarta sannan ya rufe yanaa janye da hannunta kamar bata gani ya kawota kusa da Matar Sheikh sannan ya saki hannun nata kasa kasa sosai ya ce" Sai na shigo" Dan murmushi ta saki bata ce komai ba , sai da idannuwanta ta yi magana ta hanyar yi masu kasa kasa ta dan hafe girarakinta sanann ta lumshe masa su hadi da dan kashe idonta daya a sanyaye ba a gagauce ba sannan ta bi bayan matar SHEIK dake jan hannunta tanna murmushi cike da mamaki suka yi ciki Tsaye yake yana kallon bayan mata har suka shige sannan ya sauke ajiyar zuciya ya juyo Yana juyowa suka yi ido hudu da SHEIK, wanda ya dafe habarsa da hannayensa bibiyu yana kallon ikon Allah Cire dubansa ya yi yana fadin" Yaya dai?" Sheikh ya saki murmushi mai hade da yar dariya ya ce" Ka san Allah ka kiyaye,, in ba haka ba sai ta shanye maka man kai tassssss ka zo kana kama sunnanta a fada, ka fa kiyayi yan matan nan fa" Ba shiri shima ya saki yar dariyar yana dago hannunsa ya dan shafa kansa dake cikin rawani ya karaso suka shiga tafia, Sai da suka karasa bangaren SHEIK suka shige sannan ya ce" Idan ta tsaya a man kaina kadaima da sauki, gaba daya bata jin magana , nine abin yakinta ba kowa ba, Allah dai ya rufawa maza asiri kar fita fadar ya gagare su" Daria Sheikh ya saka har yana zama hadi da dafe kansa yana kyakyata daria ASADEEK na sakin murmushi ya zauna shima hadi da dora kafarsa daya kan daya yana girgiza kai yana kallon SHEIK dake tafka masa daria harda ta keta Sai da SHEIK ya tsagaita da dariarsa sannan ya shiga tambayarsa shin yaya suka yi da HUZNAH? *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣7️⃣ Murmushi ya yi yana sake tino yadda suka yi, a takaice ya kwatanta masa yadda suka yin hakan ya saka SHEIK jin ba dadi, domin sam bai yi tunanin zata dauki abin a haka ba, koda yake kishi na saka mata yin wani abin marar dadi wani lokacin, sai dai sukkan manta wani abu mai mahinmanci, idan har namiji na cikin halin dacin zuciya yakan saurin karkata wajen da zai ji sanyi ne, karfa ta yi wasa da damarta har mijinta ya idasa karkata ga watanta?, Koda yake kishi halita ne, kuma idan ta ji zafin hakanma ba laifi bane, sai dai kar ta ringa rikicewa ta dorawa wani laifi bayan ita ba jahila bace A tausashe ya sake nuna masa kar ya ji haushinta, ya bata dama zata gane da kanta za kuma ta nemi afuwa, ya yi mata uzuri hakan ya zo mata a baibai ne A nutse ASADEEK ya ce" Da kuka kai baiwar tata, yaya kuka samu Asaraki da matarsa yau?" Fuskarsa cike da alamun damuwa ya dauko abin recodern da suka ajiye a dakin a boye ya kunnawa ASADEEK A hankali ya lumshe idannuwansa yana sauraro, magamgannunsu a cikin hali na rikicewa, magangannunsu a cikin hali na tone tonen asirinsu da laluben waye ya sace su, magangannunsu a cikin budewa kansu da kansu asirin kansu, bama irin muryar asaraki, rikicewarsa ta yi yawa, ihun an san waye shi yake yana cin alwashin ko magauci ne ya sace shi sai ya kashe shi da hannayensa idan ya fito, a dukkan bayanansu a yanzu haka sun riga sun gama tona abinda yake son ji daga bakunnansu, abu daya ne tak zai dakatar da shi da fitar da su shine wannan mata ta gidansa macuciya azaluma , maciyiyar amana kawai A hankali ya kuma saurari na baiwarta, Saima ya samu kansa da sakin dan murmushi, wato mutun akoy saka kai a uku, ihu take tana fadin shikenan abinda Umma ke fadi ya same su, tace masu su fa yi taka tsantsan ana satar mutane , nan da nan ta rikice take tonawaa kanta asiri harta da sirrin uwar gidan nata, baban rikicinta shine kar a san tana aikataa madigo, hakan ya sa a rikice take fadin ita bata taba aikata madigo da son ranta ba, hasalima Umma ce ta tsoratar da ita da danginta cewar idan bata ringa yi ba zata yi masu shari du a kashe su, a rashin hankali irin na mutun sai ta zabi hukuncin ALLAH kan na mutun, ta manta da ta kiyaye Allahn shine zai kareta, kai koda ta fada a ramin UMMA an yake mata hukuncin ta yiwu ya zamo sanadiyar shigarta aljana Dif ya kashe rocodern yana kallon gefe , a hankali ya ce" Ka san tunda Tuzuruwar kauye tacewa matar nan KWATUWA, na san ba banza ba, wai ka kuwa san harta Auta ta nunawa?" Cike da bacin ran jin haka SHEIK ya ringa la'antar aikin nan, yanaa kamanta girman zunubinsa, sannan ya yiwa Allah godiya da bata samu galaba a kan Auta da NADIRAH ba Dan tsai ya yi yana kallon SHEIK jin yace da NADIRAR, haka kawai sai ya ringa jin wutar kishi da karra jin haushin UMMA a zuciyarsa, ai kam ta yiwu itama ta so ta........, Kai jama'a sai ya ringa jin kamar ace fa mai wuya uwa marikin lema ne, da sauri ya shiga jan numfashi yana ambaton sunnan Allah, dan sai shedab ya shiga hasko masa gyaran jikin Tuzuruwar kauye da aka yi kwartuwar nan na tsaye tana kallon abubuwan dake yiwa Tuzuruwar kauye kaikayi a yanzu...... innalilahi,, kai jama'a, Allah shiga tsakaninmu da mutumen! Mikewa Sheikh ya yi ya karasa wajen wayarsa dake ta ruri ya dauko yaa dawo ya daga yana amsa salamar matarsa A hankali ya kai zaune yana furta " Alhamdulilah, Alhamdulilah, Alhamdulilah, Allah ya raba lafiya, Allah ya bata lafiyar rainon ciki..........." Yana katsewa ya kalli ASADEEK wanda harta da bugun zuciyarsa tsayawa ya yi tsakkkkk yana kallonsa Murmushi ya sakar masa tatausa, hadi da mika masa hannu yana kokarin furta kalmar dake saman lebensa ya ga ya mike tsaye gaba dayansa, sai kuma ya ga ya duba ya kai sujada goshinsa a kasa, ya dauki dan lokaci Sannan ya dago ba wata wata ya rungume Sheikh gaba dayansa idannuwansa a lumshe, kirjinsa na wani irin dokawar da ya saka SHEIK sauke hawayen farin ciki, muryarsa na rawa ya ce" Alhamdulilah ASADEEK, ka ga hukuncin Ubangiji ko?, Shine mai karewa, shine mai badawa, shine mai hukuntawa, kana raye, kana tafe, ana hakarka ba ji ba gani, ta hanyar masu hakar taka Allah ya sako sandiyar farin cikinka, ta sanadiyar masu son gannin baka duniyar kwata kwata Allah ya sake dasa dasshen da zai tabatar da kai koda ka gushe a duniyar....., Ka gani ko? A lokacin da baam zato bama tsamani, ka ga karfin addu'a da kaiwa Allah kuka ko? Shin mutun ya isa ya yi maka wannan kuwa? Babu hanyar da za'a iya kaiwa gareka irin ta matar nan, sai Allah ya ringa bata damar, ta cikin damar kuma ya sako damar kareka..... ALHAMDULILAH " A hankali ya ringa sauke ajiyar zuciya, zuciyarsa na yi masa rauni da tarin soyayar dake neman fin karfinsa, yana ji tamkar ya cirro ransa ya mika mata , yana ji kamar ya ringa ihun murna har sai ya zagaye garin nan Yana hangowa shima nan da dan lokaci idan Allah ya bara masa za'a wayi gari ya ga dan jariri da sunnan nasa............., Shi kuwa idan bai bautawa ubangijinsa ya kuma gode masa ba , me zai yi? Y ALLAH Muryarsa a matukar sanyaye da sanyin soyaya ya ce" SHEIK........, Sheikh...........ina zan kai farin cikin nan?" SHEIK da shima muryarsa a dan sanyayen take ya ce" A zuciyarka zaka adana har Allah ya fitar maka da danka ko yarka lafiya, domin ka sani ba zaka taba rayuwa babu makiya ba, wadinnan da suka bayana sunne na fili, akoy wasu wa'inda ba zaka taba sanninsu ba ta yiwu har ka koma ga ubangijinka, ka ci gaba da godiya ga Allah, sannan ka koyi taka tsantsan, ka ga, ciki ba'a yi shi dan abinci kadai ba, dole mu boye maganar cikin nan a tsakaninmu........." Ajiyar zuciya ya sauke yana sake matse Sheikh ya ce" Sai nake ji, kamar na fitar da ita har ta haihu......." Sheikh ya saka hannu ya bambare jikinsa yana cewa " Malan sasautawa tsoho mana meye haka?.............." Sasautawar ya yi yana murmushi yana kallon SHEIK dake duku duku wai ya karya shi, ya zauna yana kallonsa ya ce" Garinka fa?, Ka san idan ka fitar da ita binta zaka yi, ka sani ko a ina ne Adu'a ce zata tsareta da abinda yake cikinta, kawai aduarmu zamu nin'ninka........." Murmushi ya yi ya karasa ya zauna shima a gefen Sheikh din , a sanyaye ya ce" Sai nake jin tsorron furucin HUZNHA, da ta ce na fi son NADIRAH a kanta........., Abinda ke min yawo a zuciya na son tsoratar da ni domin ba da wasa nake jin abin ba" Sheikh na kallonsa a sanyaye ya ce" Dama, akan iya wayar gari, ka tsinci a irin wannan yyannayi, yan Adam muke, zuciyyar dake cikin kirjinmu bata da kashi, wani da sauki sauki fa, wanin fa wadda zaka ga ya dawo yana haukan so din ko girmama shi bata yi, lamari ne na zuciya da hukunce hukuncenta, abu daya zaka yi kokarin yi shine ka fi karfinta, sannan ka kamanta adalci a tsakaninsu, babu wace bata yi maka rana ba, babu wace bata sonka kaima ka sani, dan haka kowace ka rayu da ita da kulawa da gwargwadon kyautatawar da kake iya bata , kana yi kana tuna gobenka, ka ga kamar likita ne da yan uwanta, har cewa suka yi idan ranar likita ne ina tarda ita dakinta, ni kuwa ban taba kula da haka din bama, abinda ya sa nake dan zuwa wani turare ne da ita mai kanshi, bana so ta manta shi idan zata zo, kuma ita bata fiya damuwa da waya ba idan na shigo, sai na yi ta kiranta bata dagawa, a dole nake lekawa na tuna mata na koma" Murmushi ASADEEK yake dokawa, gaba daya fara'arsa ta girmama, da kyar ya iya hakurin har suka yi sallah kafin suke shigewa cikin Bangaren sirikansa suka fara nufa dan ya gaishe su Sunna shiga ya tarar da ikon Allah, tuzuruwar Kauye ta ajiye abayar da nikafin tana shan hira da kyakyata daria a gaban Innar birni Sheikh kam dakatawa ya yi daga waje dan ya san ana iya samun hakan, shi kuwa ya zauna kansa a kasa yana gaishe da Fatime, wace kunya ta sakata kamar zata nutse da girmamawa tana rankwafawa tana gaisar da shi, hakan ya saka NADIRAH sakin murmushi tana kallon Innar birni, har ya gama ya mike kansa a kasa ya fita Daria ta saka tana tafa hannu , tana juyowa suka yi ido hudu da innar birni wace ke watsa mata harara, a dole ta kama kanta ta hadiye dariyarta , ta karra fuskantar Innar Birni tana fada mata irin marin da Innarta ta watsawa Umma, da irin darun da innarta ta yi a gaban ASADEEK Du idan tace ASADEEK sai mamanta ta zabura, ama sai ta ga yar ko a ka , a dole ta cire dan ta kula Nadirah kam sauki sai na Allah kawai, ba zat kirayi Aban datawa da Aba ba!, Yanzu ta gama cin alwashin idonta idon Aminu sai ta zazabga masa mari wai ashe shi bashi da amana? Hum, ta dawo kan Auta ta ce sai ta zaneta tsoronta ta yi yawa, ita dai tana biye da ita tana wankwta daga ta yi bara baranma har ta dire kan Aban datawa Gannin dai abin sai a hankali sai kawai ta ringa binta da ido ita kuma tana daria ta ce" Allah innar birni baki ji ba da aka ce an sace ku, kamar zan summa haka na ji, kamar na haukace fa, dan kuwa a ranar na je na fada masa komai, su inna har an yi jiran rataya sai Allah ya taimakemu bai rataye mu ba" Da wannan hirarakin suka karra jimawa har Aban Birni ya shigo ya sanar mata ta fa tashi mijinta ita yake jira, nan ta nuna zata kwana a gidan, harda su neman yin birgima Innar birni a rikice ta mike ta ce" Ke kar ki jiwa abinda ke cikinki ciwo mana, Indi sai fa kin daina burgimar nan yanzu dan walahi zaki jiwa abinda yake cikinki ciwo......." Dif ta dauke wuta, a ranta wata mahaukaciyar kunya da ta sauko mata sai ta ji kamar zata nutse Ba shiri ta mike tana mayar da rufarta ta wuce zungui zungui ta bar bangaren su Innar birni bata ce komai ba, fatanta ta yi nisa dan an riga an tona mata asiri sai hakuri Yanzunma shi ya bude mata, har Allah Allah yake su koma gida ya dorata saman cinyarsa ya bata dukkan lokacinsa a haka Ta waya ya cewa Sheik matarsa ta yi masa dukkan bayanin abubuwan da ya dace a kiyaye da wa'inda ya dace ta ringa ci dan samun ingataciyar lafiyar abinda yake cikinta Innar birni kuwa kira ta yi ta dokawa har ta samu inna Hindu, ta shaida mata to fa sai an karra yin taka tsantsan, sai fa an dage da addu'a da kuma kiyayewa, daga yanzu girki idan ba ita ta yi da kanta ba sai ko in ita inna Hindun zata yi mata ko auta, kar a bata abinci ta ci daga hannun kowa, daga karshe ta shaida mata Aban birni yace UMUGHLUK ITIBEL ya bada umarnin a kawo HABU Masarautar zai gana da shi, da wannan farin cikin suka katse wayar Tunda magariba ta yi suke zaune a falonsa, a kasa watau saman cafet sun saka salak gaba ASADEEK kallon abunda take nufi da abinda zasu ci yake, salak ne da kwaki da yankan tumatur da yaji da ruwa ruwa wai mai ruwa , har fadi take ya tsaya ya dandana zai ji dadin abin Allah ne ya taimake shi kira ya shigo daga bangaren Umma, nan ya samu ya mata wayo ya silale da yajin ya rufe ta waje ya tafi da kY din bangaren Ummar Yana zuwa ya tarar da ita zaune , cikin shigarta tun ta safe, ta yi wani firi firi da ita a saman kujera yan fadar tata uku a kasa a zazaune kowace alamun tashin hankali ya gama bayana a fuskarta Kuka ne ta fashe masa da shi, bayan sun gaishe shi sun basu waje tana saukowa kasa hankalinta tashe ta ce" Yarona, ko dai ka samu matsala da wani ne yake harin dukkan wani dake gefenka dan ya halaka?, Ka ga babu bafanka da matarsa , dama tunda na ji haka hankalina ya ringa tashi ,na san daga su sai ni kake da shi a duniyar nan iyaye, ka ga dazu na aiki babar hadimata , har yama bata dawo ba , sai na saka a bi min sawu, aka sheda ai an ga an dauketa, wayo na shiga uku yanzu nice ake hari kennan?,dan Allah ka baza min masu tsaro ta ko'ina dan kar a dauke maka ni" Da kyar ya iya ba kansa hakuri ya danne abinda ke taso masa, sai yake ji har wani karni take yi walahi, ko yaya aka yi a da baya ji? Cike da nuna damuwa ya ringa salalami yana kama bakinsa, ya mike yana kai kawo ya fuskanceta ya ce" Umma, ni ban samu matsala da kowa ba, hasalima ni na fi tsoron ko su bafa ne suka samu matsalar da wani? Ama ai karya ne a shigo a dauke ki, hana dai,an dai tarbi na waje , ba dai Uwata ba!" Yannayinta a tashe ta ce" Yarona, cewa aka yi wani irin katon mutun ne ke dauke mutanen fa, kar dai aje yan garkuwa da mutane ne, ko yan yankan kai, tunda ai Revell namu ne ko?" Danne zuciyarsa ya yi ya ringa nuna mata ko su waye zai samu bakin zaren, yanzu yanzu kuma za'a kawo mata masu gadi,kar ta yarda ta fito daga bangarenta, ta yi zamanta da hadimanta har ya samo bakin zaren Da wannan ya kwontar mata da hankali ya fice a bangaren nata Bangaren NADIRAH ya nufa Daga kofa ya nemi izinin shiga , hakan ya saka Auta dake waya tana doka murmushi zuwa ta bude Tana gannin yayanta da sauri ta zarro ido hadi da neman boye wayar, dan ya hannata ai waya da mijinta Hannun nata ya bi da kallo, sai kuma ya dauke kansa ya yi murmushi, kasa kasa ya ce" ki gaishe da Inna, plz ki harhada kayanta a bani ta baya, dan bana so tana yawo da yannayinta....." Auta na murmushi ta amsa shi Shima yana murmushin ya juya, har zai tafi ya dawo ya dan dakata yana dan ragewa idannuwansa girma ya ce" ki ce masa, kusan sati bai kirayeni ba ko gaba muke?, Sannan ki ce masa ya zo ya dauki Matarsa dan Tuzuruwar kauye tace maza a mayar mata da ya gidanta....." Daria ce ta fashe da ita har tana rike ciki, shima ya juya yana doka murmushi ya fita ya nufi bangarensa yana daga waya ya yi kiran Sheikh A nutse ya sanar masa muradinsa, watau a saka sarkin yanka ya dora yaransa hudu bangaren UMMA, dan yana da bukatar sheda, yana matukar son sheda irin ta musulunci, ba zai iya dora mata laifin Madigo kai tsaye ba, sai ya kamata da shedu ta yadda zata fuskanci hukuncin da ya dace da ita................. Wannan kennan A hankali rayuwa ta ci gaba da tafia, a cikin sati uku harta Auta an shiryata Inna Hindu ta rakata dakinta, a censai da ta yi mata kwana hudu sannan ta gudo dan kuwa sai da ta zauna kusa da ita ta sake shiryata zama a cikin ahalin da aka saka masu tsanarta ta hanyar kage da karya kala kala A tsayin lokutan kuwa, wadinnan mutane sunna cikin halin rayuwa, halin rayuwa mai tafe da tashin hankali, babu isashen barci, babu walwala babu cin abinci yadda ya kamata, tun daga matar sarkin Dogon dutsi da yaronta, da sarkin tanus da matarsa da yarsa wace ke neman haukacewa kan soyayar balarabenta tana dudurawa du wani mugun da ya sace su ashar da tsinuwa da Allah ya isa, a gangaro kan baiwar Umma, da Umma da hafimanta , wa'inda suka dinke a cikin daka suke fama da zukatansu babu dare babu rana, zaman waje daya ba nasu bane du a kuntace suke da halin kila wa kala ................................................. Yau ta kama talata ce, tunda safe Umma ta sha maganin barcin da take ba Auta dan ta samu barci, ta maku ta je daki ta yi kwonce take barci tamkar mataciya har sai da yama ta yi magariba ta kusan shigowa ta dan motsa tana bude idannuwanta da kokarin tashi dan barcin ya saketa Kasa kasa ta ringa jiyo nishi, da gurnani irin na iya shege, hakan ya sakata jin tsammmm nan da nan jikinta ya shiga amsawa A dan zabure ta iya mikewa, ko ido bata wanke ba ta fito tana wara idannuwanta dan jiyo abin take sai karra shigarta yake yi,rabonta da wannan lamari fa a kadan an yi sati uku da kwanaki A kan hadimanta biyu idannuwanta suka sauka, sun dage a cikin aiki irin wanda suke yi yau da kulun sunna yiwa junna shirme irin na Madigo, dayar kuwa a gefe ita ke kokarin taimakon kanta da wani salon masifar ta bata kai da fata tana yi Nan da nan tsumi irin na aikin da aka saba ya motsa mata Daga tsayen da take ta ringa cire suturarta har ta idasa cirewa tasssss sannan ta karasa cikinsu ta rabasu ta yi daidaya ya zamto su dukansu sun rufu a kanta dan bata nata taimako ta hanyar yadda badalarsu a tsakaninsu A irin wannan lokacin ne, yaran sarkin yanka dake labe tun farawar yaren Umma sunna dauka a waya, suka idasa dauka sosai da sosai sannan suka dauka harda su din watau sunne shedu hudun da ake da bukata kafin suke bayana masu kawunansu ta hanyar shigowa kai tsaye suka kashe fitila, sannan suka sake kunnawa A haukace hankalinsu ya dawo gangar jikinsu, hadi da bugawar zuciya mai tsananin gaske Lokaci daya zufa, da murdawar ciki suka wanzu a irin wannan lokacin, daya ya juya ya fice da abinda suka dauka, ya rage ukun nan dake tsaye fuskokinsa babu alamar sun taba sannin menene dariya a duniya Jiki na rawa, fata a yamutse na alamun tsufa ya fara salamowa, Umma ke wawure wawure tana son warto zanninta dan ta rufe yamutsatsiyar fatarta da kwasha kwashan nonuwanta da suka yi la'asar tana furta" Innalilahi wa inna ilaihi rajune meye wannan, ku kuwa su waye ku? Me kuke so? Yaushe kuka shigo? Waye ya barku kuka shiggggggg" "Ke dilla rufe mana baki algunguma mai dati ko mu lalata maki fata yanzun nan, ku kuwa du wace ta kuma gwada mikewa sai mun kakarya mata jiki kafin UBAN TALAKAWA ya zartar da hukuncin da ya dace a kanta!, Tsitttt bama son mugun motsi ko mu motsa maku jiki shashashu mararsa tsoron Allah masu yada fasadina doron kasa a tsaftataciyar masarauta!" Ya daka masu tsawar da ta saka dayar sumewa, lokaci daya kuma su UMMA aka shiga hali na tabuwar hankali da gigicewar yannayi......... Sake yinkurawa ta yi, a lokacin da ta tuna me yace, yana nufin zasu sanarwa UMUGHLUK ITIBEL wannan aiki, aikin da baya dagawa kafa, mugun aiki mai wuyar sha'anin,aiki mai zafi mai ci masa tuwo a kwarya, wanda ya yi rantsuwar ko shi ya faru da shi sai an jefe shi tunda yanada aure, bale wani nasa ko talakawansa, aikin nan da ta tabata idan aka kai masa rahoto babu mai kwatarta ko waye ya sakata motsawar, hankali tashe ta rikito kasa tana hade hannayenta, bakinta na bari cikinta sai kugi yake zata yi magana aka budo kofar aka shigo, shigowar da ta kunce mata ciki yararin abu ya shiga bin jikinta, mai ruwa mai tsami mai kalar kore, lokaci daya kuma ta ja numfashi tana bin fuskar wanda tunda ya shigo bai kalli inda suke ba, saima umarnin da ya bada da hannunsa cewar a basu sutura, dan sannin girman tsiraici da ya yi da kare idannuwansa kallon dati da yake yi, sannan ya juya bai ko dubeta ba, ita Ummansa ya fice......lokaci daya ta tafi kasa numfashinta na barin gangar jikinta! Takensa kennan, Namiji son gannin mai halayar kirkidauke numfashin marar gaskiya Takensa kennan UMUGHLUK ITIBEL bawan Allah mai kare dokokin Allah Miji a wajen HUZNAH DA NADIRAH Uba a wajen AUTA Idan na ce maku saura kiris kun yarda?😁😁😁😁 *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣8️⃣ Jiki ba karfi ya haye saman bed din da NADIRAH ke kwonce tana kallo a wayarsa tana murmushi A hankali ya sanyo hannunsa ya zagayo saman cikinta ya dora sannan ya lumshe idannuwansa , kansa a wajen wuyanta, Dama HUZNAH yanzu sati kusan hudu kennan rabonta da zuwa inda yake, tunda aka yi abin nan ta sheda masa tana so ta samu lafiya koda zata ci gaba da daukan kwana, wai dan koda ta dauka a yanzu ba wani anfani zata iya yi masa ba Ya nuna fushinsa a kan hakan , ya tarda ita har bangarenta, ama ta nuna tana so ne ta kula da lanta sosai, ya yi mata wannan alfarmar, a dole ya kyaletan, dan kansa bashi da space din sake daukan wani matsalan ko kadan A hankali ta ajiye, ta juyo ta fuskance shi, ta tsurawa fuskarsa ido Dama tunda ta ga ya mike a zabure ya fita ta san da wani abun Ita yanzu har fargabar ya fita ya dawo da wannan yannayin take Sam baya iya dane damuwarsa a gabanta Yanzu gaba daya fuskarsa ta dauki jajajir , idannuwansa kuwa sun kankance sosai A hankali ta ce" Menene?, Waye ya taba min kai na je mu casu?" Idannuwansa dake lumshe ya dan dago a hankali yana kallonta, dan murmushi ya yi yana kallon idannuwanta, muryarsa a shake ya ce" NADIRAH......, *INA SON KI*" Dum gabanta ya buga, aa hankali ta ringa lumshe idannuwanta har ta zubawa lebensa ido Numfashi ta ja kadan sannan ta idasa shigewa jikinsa A sanyayen ya ce" Dan Allah, ki so ni domin Allah, sannan ki rike min mutuncina....., Idan a zamantakewar aurataya da muke yi ni da ke, akoy wani abu da kike so na yi maki wanda bana yi, ko menene, in dai bai taka dokar adinin musulunci ba, watau zuwarwa mace ta dubura....ki sanar min, ko ki kwatanta min....., Ba zan taba jin kyankyaminki, ko kiwyar yi maki ko menene ba, dan Allah kar ki dubi wani ko watana, hakan zai iya tsayar da numfashina NADIRAH......" Yana fitar da huci ya karashe maganar, ya dora da fadin" In ba jaraba bama, meye za'a tsinta a dan uwan halita, ina zumudi da son gannin kwaf, ina abinda zai shigeka ya gigitaka?, Shikenan kaine wawa sakarai ka zo ka amshi iri irin naka? Allah ya wadaran naka ya lalace!" NADIRAH dake ta danne dariarta, dan a bayane ta fahimci kishin mijinta ne ya motsa sakamakon wani abu da ya gani, tana kyautata zaton abin a waje ya gano shi har ya rikitashi haka, sam bata yi tunanin ya shafi Umma ba, shi yasa take dan murmushi ta ce" Ai kam, wai ka ga kwarata mata, kuma ka ga maza na mu'amala da maza, nima na sha ganni harma wata ta taba nunan wai inada kyau" Raunanun idannuwansa ya zuba mata, a hankali ya ce" Bakya tausayina?, Kina gani fa hankalina a tashe, matar cen ne fa aka kama yau dumu dumu cikin alfashan nan, dan Allah ki daina mana" Sai a lokacin ta gane, a hankali ta shiga nuna masa bata gane bane, ya yi hakuri, sannan ta shige jikinsa tana dan dora hannunta a saman kirjinsa Ajiyar zuciya ya sauke, a sanyaye ya ce" In sha Allah, za'a fitar da su dukansu sati nan da zai kama a zartar da hukuncinsu" A hankali ta dago tana kallon fuskarsa, muryarta a sanyaye ta ce" Kashe su za'a yi ?" Fuskarta ya dan zubawa ido, sai kuma ya sauke yar ajiyar zuciya a hankali ya ce" Kina tsoron gani ne?" Da sauri ta gyada kanta , hakan ya saka shi yin dan murmushi ya ce" Idan za'a yi, za'a shigar da ke, domin ya zama dole a ranar ki fito da shigar Alkyabarli, ke da yar uwarki, dan kuwa a gaban kowa za'a zartar, ama idan aka zo gabar mumunan hukunci wanda yake da rauni ba'a matsa masa kallo Gaba daya sai ta ringa jin shayinsa, da tsoronsa a zuciyarta, wani girmansa da kiyayeshi ya rinha ratsata, a wannan daren du irin jarabarsa bai nemi komai a wajenta ba, itama bata gabatar masa da komai ba, dan ta kula lalle fa ya shiga lokaci na bukatar tunani da zuciyarsa A washe gari cikin baban gida da zagaye, da cikin gari ya dauka na rufe UMMAN ASADEEK da ka yi Kafin kace meye wannan Fada ta fara neman dinkewa da baki, sai da aka dakatar da ziyarar kowa , ba baba ba yaro, ba na kusa ba na nesa, haka kuma aka zuba masu tsaro a ko'ina, bama irin bangarensa da na HUZNAH , da na NADIRAH A hankali kwanaki ke karatowa, har ranar da aka tsayar da gabatar da hukuncin nan ta zo Tunda garin Allah ya waye baban fili na shara'a ya cika makil da al'uma, dan kuwa har daga wasu garuruwa an zo kallon shara'ar nan, manya manyan sarakunna kuwa daa kusoshin gwamnati sun zo dan halartar shara'ar, manyan alkalai na gwamnati da na musulunci sun zo dan summa a yi shari'ar nan da su, wace za'a yita da sanyin safiyar ranar, ya zamana wajen tuni ya dauki harama , jami'an tsaro na gwamnati da dogarai kuwa sai sake tsara wajen suke sunna daidaita tsaron wajen Lokaci na yi ya zamana waje ya gama dinkewa, kusan kowa ya fito banda mai martaba da matansa, a ka'ida kuwa sai sun fito zai fito, ko kuwa su fito tare A hankali suke tafe, bayan an basu damar fitowa daga bangarenta dan nufar na HUZNAH, wace tale uwar gida, ya zama wajibi sai sun je bangarenta sannan su fito tare, domin su din iyayen al'uma suke, babu wata rana da zasu fito gaban al'uma kawunnansu a watse, ko wace iri ce kuwa Daga sama ta sauko, bayan an sanar mata tana iya saukowa sun karaso Itama shigarta Alkyaba ce mai tsadar gaske, bambancin alkyabar nasu color ne kawai, bayanshi komai na alkyabar nasu su biyu iri daya ne, kasancewar mai shiryasu ta cikin gida ta shirya su ita ta dauko haka dan su saka Tunda ta sauko, da farko yannayin fuskarta a dinke yake, du irin yadda ta yi yaki kar ta nuna kishinta da farko sai da ya falasata Sai dai ga mamakinta, a yau, maimakun ta ji kalamai masu zafi da neman shiga hanci da kudundune daga bakin NADIRAH, sai ta ga bayan sun yi ido hudu na farko tana kare mata kallo, a na biyu sai ta ga ta sakar mata lalausan murmushi sannan ta wani irin risinar da dubanta tamkar sarauniya hanshakiya a tausashe ta furta" Barka da fitowa, Aunty" Murmushi Auta ta yi ta dauke idannuwanta ta cira kanta, cike da wani irin takama da isa irin na jinnin dake yawo a jikinta, hamshakiyar yarinyar mace mai cike da gayu da jinnin sarauta a jinninta, wace take takama da ikon Allah da kuma yarda da amincewar miji ta dan sake sada dubanta kasa kasa ta furta" Barka da saukowa aunty........." Sai kuma ta kalli NADIRAH dake dan kallon hanyar kicin tana ta danne damuwar dake ranta na tarin tsoron abinda zata iya ganni a yau, hasalima rabonta da mijinta kwana biyu cirrr yau, sai dai ya zo ya ganta a bangarenta ya rungumeta a jikinsa, ya kuma tafi, haka ko zuwan ya yi wani dari dari take kallonsa, gaba daya wani bako ne da take son sani a gabanta a yanzu Tana murmushi ta mike tsaye ta ce" Momyn Autah mu tafi , auntyn ta sauko" Ajiyar zuciya NADIRAH ta sauke ta muke itama, tana jan alkyabarta dan rufe dan karamin cikinta, wanda du wanda ya santa a da da irin lafafen cikinta idan ya ganta a yanzu kallo daya zai gane ta dauko , in kuwa manya ne masu baiwar sani sunna kallon fuskarta zasu gane tana da wata kama A hankali ta koma wajen da aka nuna mata ta tsaya, HUZNAH kuwa ta dan sake zuba mata ido sannan ta daga kafa a hankali suka shiga takawa kowace da nata kalar izar sun saka Huznah a tsakiya har suka karaso wajen zamansu, suka zauna karkashin rumfar da ASADEEK zai zauna, wace an dai tanadeta ne ama ba asalin zaman zai yi ba dan baya zama sam idan yana shara'a Mintuna ƙalilan tsakani aka shiga shelar fitowarsa Gaba daya sai da tsigar jikinta ya tashi sakamakon gannin dukkan wani sarki ya mike yana kallon hanyar da zai fito A hankali ta kai nata idannuwan itama bayan ta mike tsayen tana kallonsa ASADEEK ne wannan Mijinta ne ita yar HINDU Shine ke tahowa tamkar dawisu Shine yake doso su tamkar rana Takama a cikin tafiyarsa, girma da daraja a tare da shi Ya dauki rawani mai girman gaske, suturar jikinsa ta jinnin sarauta ta dauke idannuwan dukkan wani mai kallonsa, hannunsa rike da sanda irin ta saraki yana tafe da ita a nutse har ya karaso wajen sarakunann dake tsaitsaye cikin girmamawa ya gaishe da su, baban yaronsa wanda yake tafiya kasashen waje da shi yana ta faman gyara masa kayansa , SARKIN YANKA yana tsakiyar fili a tsaye, hannunsa rike da sharbebiyar wukarsa, wanda da yawa basa son kallonsa dan tsoro yake basu, SHEIK na gefen ASADEEK hannunsa rike da Alkur'ani mai girma da fari kal din carbi, cikin shiga ta manyan malaman adini ya nada hirama a saman kansa Bai karasa wajen da zai tsaya ba sai da ya gama gaishe da kowa cikin mutuntawa sannan suka karasa wajen da zai tsaya ya yi tsaye yana kallon abun da yaronsa ke gyarawa wanda zai makala masa a kunnensa ya taho kusa da bakinsa dan idan ya yi magana kowa ya ji shi Idannuwa ne suka sauka a kan motocin da suka ringa shigowa da masu laifi, hakan ya sa shima ya zuba nasa idannuwan har suka gama karasowa suka layu Idannuwansa ya sada, a hankali ya rufe amsa amon yana kallon SHEIK, muryarsa a sanyaye ya ce" MAI DAMAGARAM ya zo taron nan?" Sheikh ya amsa shi a tausashe yana kallon yannayinsa A hankali ya ce" Ka taimaka, ka sanar masa cewa, shi zai zartar da hukuncin da ya dace a kanmu baki daya, domin ba zan iya magana mai tsayi ba, ba zan iya ba" Sarkin Yanka dake ta shawagi ne ya kallo wajen, sai kuma ya dauke kai, dn jinkirin nan dama ya san da wahala idan har ASADEEK zai yarda da maganarsaa, ama ba komai a zartar dinma zai fi Nan da nan aka kai bayani wajen Mai DAMAGARAM, wanda ya zubawa ASADEEK din ido shima, zuciyarsa na tsintsinkewa da tunanin da shine yaya zai ji? Ba ja ya mike ya amsa gayatar nan ya karaso wajen da zai saurari komai tare da neman alfarmar duk wani sarki ya shiga lamarin dan a hadu a yi abinda ya dace A lokacin aka ringa fitr da su baki dayansu Da farko du a gigice suke kale kallen filin da jama'ar dake zagaye Furucin aban Bahija ya saka su tsurewa summa a lokacin da ya furta" Shikenan, tamu kuma ta kare" yana kaiwa zaune ya sada kansa jikinsa gba daya na rawa tamkar mazari, a lokacin ne kuma ya'yansa da suka halarci taron suma suka rikice waje ya nemi hautsinewa Da kyar aka iya daidaita wajen da iface iface da koke koke da rikicewar masu laifi , zan iya cewa saima da SARKIN yanka ya doso su rai bace Bahija ta zauna tana rukunkume mahaifiyarta tana tsagewa da kuka tana sake hango mutumen da ba zata taba manta fuskarsa ba domin sun hadu ne a saudiya da masoyinta, shin me ya kawo shi nan? Ina masoyin nata? Kar dai shima ya zo kallon shara'ar nan ce da sam ita bata daga mata hankali dan kuwa du tsuntsun da ya ja ruwa , ruwa ya dake shi malan!, Ama ba zata so ya ga haka ba dan ba zata so wani abu ya faru da soyayarsu ba, ko me zai faru da iyayenta ta san mai tsauri ne, domin ita bata san wasu abubuwan da suka aikata bama sai a rufe sun nan da aka yi, walahi idan ya kama zata fito ta fadi abinda ya faru , ba abinda ya sha mata kai, mahaifinta ya yi nisa, ita sai da ta dawo kwana a zaune kar aje ta yi barci ya kasheta itama, irin yadda abin duniya ya sayi zuciyarsa komai yana iya aikatawa A hankali aka shiga gabatar da addu'a, kowa yana amsawa, SHEIK na zubo adu'o'i har ya kai karshe A tausashe ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 6️⃣9️⃣ A taisashe Sheik ya ce" Alhamdulilah, muna godiya ga Allah da ya nuna mana wannan rana, muna rokon ALLAH ya bamu ikon zartar da sha'ar nan bisa adalci, ya hannemu sin kanmu koda na second daya ne, ya kuma sasauta mana zukatanmu, ya sanyaya mana su , ya yafe mana kura kuranmu, alhamdulilah, zamu gabatar da abinda ya tara mu a nan dan kowa ya tafi uzurin gabansa" Daga nan ya juya wajen Mai DAMAGARAM ya dan risina da girmamawa ya bashi waje ya koma gefe ya tsaya Takardar daake hannunsa yake dubawa na tsayin lokaci, a kadan ya dauki mintunna ashirin yana yi, dan kuwa harka ce ta shara'a ba kawai zai hauta ba duda aikinsa ne A tausashe ya dago yana duban kowa , daya bayan daya A matukar tausashe da girmamawa ya bada umarnin a daukowa ASADEEK kujera, domin shi dake tsayen nan har juwa ke kwasarsa, ina ga ASADEEK? zuciyarsa ta girgiza ainun, hankalinsa ya matukar tashi, a sanyaye ya kai dubansa kan Bafan ASADEEK, ya dora kuma kan UMMA, sai ya samu kansa da sada kansa a hankali yana furta" Innalilahi wa inna ilaihi rajune........" Ya yi haka ya fi a irga sannan ya dago ya fara magana a hankali, sai kuma salon maganar ta dauki zafi, har ya zamana ya dane takardar da hannunsa na hagu yana bayani a kan girma da darajar zumunci, tamkar zai kife abin ya je ya kikifawa masu laifin nan mari, da irin girman amana da laifin wanda ya ci ta! Sannan ya dawo wajen da muryarsa ta yi rauni ainun, laifin kisa, ya kuma gangaro kan aiki mai muni irin na zina da LUWADI DA MADIGO....., Karshe dai dole muryarsa ta ringa rawa har sai da ya sada kansa ya dauki tissu din da aka bashi yana dan share hawayen da suka gangaro masa, sannan ya dago a kausashe yana duban jama'ar dake wajen ya ce" Dole zamu zartar da hukunci daidai yadda adinin musulunci ya tanadar, domin tun kafin a kawo zamanin hukunci na gwamnati ake yin na shara'ar musulunci, mun yarda cewa babu makawa sai mun mutu, idan mun mutuwa kuwa zamu tsaya a gaban wanda ya halicemu, sanadiyar wannan na tsaya a yau a gabanku sannan ina mai rantsuwa da wanda raina yake hannunsa, babu wanda za'a cuta mu ji mu kyale dan yana dan uwanmu, mahaifiyarmu, mahaifinmu, matarmu, yayunmu, kannenmu, aminanmu, ko wani mai fada a ji mu tauye hakin wanda aka cutar saboda shi ba, domin mun san cewa akoy ranr da zamu mutu, mu yi kwonciyar kabari, mu kuma tashi gaban wanda ya halicemu, ya umarcemu da mu yi adalci babu wanda zai saka mu a uku ya lalata mana kiyamarmu ko wanene!" Gaba daya sai da wajen ya dauki muryarsa, hakan ya sa aka karra rikicewa, bama masu laifin da danginsu Takardar ya janyo ya sake budewa A kausashe ya ce" SHARA'AR da UMUGHLUK ITIBEL ya gabatar shekaru bakwai da suka shige na dan gimbiyar Tanut, aka wati gari basa nan, yanzu an same su, shara'ar da ya zartar zamu zartar da ita a nan a yau, a kuma yanzu! Ita kuma da ta take mana doka ta dauke shi ta gudu da shi alkali ya yanke mata hukuncin kaso na tsayin shekara biyar a gidan yari dan horonta da kuma horon masu hali irin nata kan kiyayewa da yi mana haye a kan lamarin shara'ar, idan da mai magana bismillah muna da minti biyar ana iya ja da haka ama babu maganar daukaka shara'ar domin tsohon hukunci ne da aka yarda da shi, bisa laifinsa na haikewa matar dan uwansa ya yi mata fyade ya kuma kasheta!" Shiru ne wajen ya sake dauka, sai kukan gimbiya da ya cika waje tana kallon wajen da mijinta ke hakimce, wanda ya dauke kansa ya mayar wani wajen, domin ba zai taba cewa koda A bane a kan hali irin nata, ya yi mata uzuri na farko, ya yafe mata na biyu a yanzu kuma ta yi abinda babu huruminsa a ciki, tabas gaskiyar mai damagaram ne, ko me suka shuka fa zasu je su girbe shi ne, idan suka yarda wani ya lalata masu goben su me suka ci riba kennan? Allah ya sa hukuncin nan ya zamo sanadiyar yafewarsu a wajen ubangijinsu, sannan ya zamo ishara ga sauran al'umma Lokacin da ya dauka na shigewa ya sake bude takardar ya sake dagowa ya Kalli ASADEEK, ga kujerar nan an kawo masa ama ya kasa zama, a tsaye yake hannunsa daya a bayansa a jimke, dayan kuwa a saman sandarsa yana kallon mai Damagaram din shima Da ido ya masa alamun ya zauna mana?, Shima da idannuwansa ya lulumshe masa sannan ya dan girgiza kansa Numfashi ya ja ya sake daukan magana kamar haka" Muna da kara, shigowar kara, ta bawan Allah, wanda aka cutar, ya rubuto kara da kuma hujojinsa a bayane, WA'INDA idan wa'inda ake kararsu sunna da musu a kan haka sunna iya yin magana a kowani irin lokaci su musa, sai dai su sani munna dauke da vidios, da kuma recoding muryoyinsu wa'inda ke tafe da tabacin karar mu, in sha Allah zamu fara daga kan Laure sannan mu karasa da Asaraki" NADIRAH da jikinta ke rawa, zufa na keto mata ta kalli Auta, muryarta na rawa ainun ta ce" Innalilahi wa inna ilaihi rajune, kar ya fadi Auta, dan Allah a zaunar da shi, ban san in har zai iya jurewa ba, yana yi kamar ba komai ama ki dubi yannayinsa , Auta ki dubi yannayinsa......" Sai kuma ta kalli Huznah, a rikicenta ta ce_ Aunty, ki saka mijinki ya zauna, dan Allah ki dauki maganana da mahinmanci, ki kuma yafe min abubuwan da na ringa yi maki, ban maki su dan na wulakantaki ko dan na nuna maki iyakarki ba, hasalima ni din ba kowa bace face wace nima kadara ta biyo ta kaina, ban zo rayuwarki dan na tarwatsa maki farin ciki ba, ki sani na shigo ta rayuwarki ne dan Allah ya kadarta min, Aunty na ringa yi maki abubuwan nan ne dan ina maki hannunka mai sanda, dan ki farka daga irin mu'amalarki da mijinki ki karra kusanta kanki da shi, ama a yanzu ba zan iya jurar gannin wani abu ya same shi ba, idan har aka shige shara'ar cen komai na iya samunsa, Aunty ina iya mutuwa a kan damuwarsa....." Ta idasa kuka mai tsuma zuciya na balewa daga bakinta, wanda du yadfa ta so rike shi sai da gunjinsa ya kawo inda ASADEEK yale tsaye Idannuwansa dake da nauyi ya daga ya dora a inda suke, a hankali zuciyarsa ta buga da bugu mai tsananin gaske, A tausashe ya kai dubansa wajen Mai Damagaram, so yake ya ce da shi a shigar da Indi cikin gida,ama ya gaza, domin bakinsa ya masa nauyi sosai Shi kuwa Mai Damagaram a hankali ya dauke dubansa, domin ba zai yiwu a shigar da ita gidan ba, sai dai a yi hakuri, dole a gabatar da shara'ar tana wajen HUZNAH kuwa, lokaci daya magangannun suka ringa dukkan kirjinta da hayacinta baki daya Kukan da NADIRAH ke yi kanta a saman kafadarta ya rikitata har ta rasa me ya dace ta yi A hankali ta saka hannunta ta tare Auta dake son mikar da Nadirar dan ta wuce da ita ciki, sannan ta dora hannunta a gefen fuskar Nadirah a hankali tana dan shafawa, muryarta a raunane ta ce" Ki nutsu mana, ki daina kuka, ko so kike ki yiwa babynmu ilah ne?, Ki dubi mijinki, a yau ki karra tabatarwa SARKI kike aure, a dole mijinki ya yi hakuri, a dole ya shanye damuwarsa, a dole ya hadiye kowani bugu, a dole ya iya jure koma menene, kin ga dubi mijinki nan yake kallo, ki dago ko hankalinsa zai kwonta mana?, Ki taimaka mu bi shi da addu'a, ita kadai ce abinda yake da bukata daga garemu............" Hannunta ta saka cikin nata ta jimke, sannan ta maido dubanta idna yake tsayen yana kallonsu A hankali ya sanyayar da dubansa, sannan ya dawo da hannunsa dake jimke a bayansa ya ware shi ya dora a kirjinsa, sai kuma ya safa kansa gaba daya sannan ya dago ya sake sanyayar da dubansa, kafin ya maida inda Mai Damagaram ya ci gaba da magana A harzuke, a kuma tausashe, a hasale a kuma garaje Mai damagaram ya ringa fadin laifukan Umma, tun kafin yayan su girma, har ya kawo wajen rasuwar GIMBIYA, ya fadi cewa laifin UMMA shine ta ga lokacin da Asaraki ya zuba guba ya bada aka ba Gimbiya, ta kuma ga lokacin da take fitar rai har ind ata mutu, ta kama y'arta ta kule a daki , wato ta yi shiru tama yi farin cikin haka, dan dama so take a bata waje! Ya dora da fadin irin azabtar da Auta da ta ringa yi, ta hanyoyi daban daban Zuwan HUZNAH cikinsu, maganin da ta ba Huznah a cikin lipton wanda ya saka ta samu cuta ta rashin gamsar da mijinta, ake tafe a haka, da irin zaluncin da take gabatarwa a cikin masarautar, da auren Auta, da irin cutar da Auta da ta yi, zuwa neman auta da Madigo, da rabata da gidan mijinta da ta yi, zuwa maganar Aurensa da aka ce za'a bashi yar sarkin Tanut da aurensa da ya juye kan NADIRAH wace aka nunota da irin abinda aka dora mata kan zuwanta fadar, irin sakota a gaban da aka yi, irin gwagwarmayar da ta fuskanta, irin yadda Umma ke kawo mata magungunna ne menene burinta daya ne dai a kashe wannan bawan Allah da yake tsaye a kan dukkan uzuririkanta, yake kiranta da sunna mai daraja, yake yi mata biyaya, ta makantar da shi da matsalolin cikin gidansa, tana neman ransa ido rufe, bata duba halaci, adalci , amana da suka yi zama tun tana baiwa irin ta siye, ta dawo ta zama babar hadimar gimbiya, karshe ta zama UMMA a wajen MARIYA da ASADEEK , ta take ta murje ta lalata ya'yan mutane da yawa ta hanyar sako su a aikin madigo, sannan ta zamto ta hannun damar Asaraki.........., A rikice HUZNAH ta kalli NADIRAH dake kallon ASADEEK A rikice ta ce" Dama abinfa kike son na gani kennan na kasa gani?" Auta dake share hawaye ta kalleta itama a lokacin da HUZNAH ta kalli Auta a rikice ta ce" Dama ke ba mahaukaciya bace, dama kema tana son sai ta aikata masha'ar nan da ke?, Ashe dama abinda yake faruwa kennan idannuwana suke rufe nake ikirarin ni mai miji ni mai kishi ni mai son miji?, Mijina na cikin wannan hali na kasa gannin komai na kasa bashi talafin komai har bake ikirarin na masa adalci na zauna da shi tsayin shekaru bayan babu aurataya a tsakanina da shi yanzu ya min kishiya zai watsar da ni? Ashe nice ya ji kai yake tausayawa yake rike da ni domin Allah? Lalle babu marar hankali, marar tausayi, marar jin kai, wace banda kanta babu abinda ta sani irinta a duniya, a hankali hawaye ke zirara ta cikin idannuwanta, muryarta a raunane ta rungume NADIRAH a jikinta tana fadin " Innalilahi wa inna ilaihi rajune, tabas babu irin rikicewar da bata sameni ba sakamakon shigowarki rayuwata, ashe ke din adala ce, mai jin tsoron Allah ce, mai kuma sonmu da zuciya daya ce? Dan Allah nima ki yafe min irin abubuwan da suka ringa faruwa a tsakaninmu, ciki harda zarginki cewa ke kika min maganin rashin lafiyana bayan baki jima da shigowa rayuwana ba da ta mijinmu, Auta dan Allah ki yafe min kema, na gabatar da huldarmu a hali na ban damu da ke ba, ni in ba mijina ba babu ruwana da kowa nasa ko ke ce, son zuciyata ya min ilah, na dauki shakara da shekaru ina cutar da shi, a yanzu da ya samu lafiya nake son in kara wulakantashi da girmanshi da darajarshi? Ya Allah ka yafe min wannan kuskure nawa, yanzu da kema muguwar ce da shikenan kin gama da mu domin nu kishina bai barni na ga wacece ke ba, mijinmu kuwa a ranar farko da kika shigo matsayin matar aurensa kika tafi da dukkan wata nutsuwa ta kamewa wata macen da ba ni ba , watau ya kamu da soyayarki, wannan shinema dalilin da ya sa na sake kulatarki dan ban saba ganninsa a halin begen wata da binta da kallo bayan ni ba........" A dole suka katse sunna sauraron hukuncin Umma, wanda ya sa ta sake saka ihun kuka tana sake zubewa kasa, ace ita Umman Asadeek yau an wayi gari za'a yi mata bulala dari a bainan nasi, sannan a wuce da ita gidan yarin gidan nan daurin shekarun da ta tabata sai dai gawarta dan bata tashi auna shekarun da nata ba sai da aka sanar mata cewa zata yi su ta gane da wahala ta maimaita su a duniyarta, itace zata je waje mafi kaskanci mafi rikita tunanin bawa ta rayu a cen tana hangen yar bayi a matsayin matar ASADEEK? Itace zata wayi gari ba uwar ba ribar,? Take ta ringa jin wani irin suka a zuciyarta mai tsananin gaske tana gannin yadda yaranta ke ihun kuka sunna kallon bulalar dake hannun Sarkin yanka tafkekiyar da ta tabata daya tak ta isa ta kunce notikan kanta baki daya ta kasheta, itace za'a zazabga masu, sai dai dama dama su, sunna da damar wata rayuwar, itace tata ta kare, ta sani ba zata taba yin tsayin rai ba a gidan yari, ba zata iya ba, idan ta je ta samu mutanen da ta aika gidan yari su kadai sun isheta UKUBA A GIDAN DUNIYA! N asaraki aka bude, shafinsa mai tsayin gaske, wanda sanadiyar wannan aiki nasa harta rayuwar garinsa sai da ya ja aka bincika Da aka fara zayanowa sai da ya'yansa suka ringa silalaewa daya bayan daya sunna guduwa, dan sai sukka fara jin tsoron kar aje shafi ta shafe su, wannan masifa da me ta yi kama? Lalle da ake cewa giyar mulki na haukata wasu to fa wannan ta haukatar da ubansu da kuma matarsa mai taya shi, inda Allah ya taimaketa bata san da maganar kisa ba sai da ya sanar mata a gidan yari, laifinta na taimakawa ne kawai wajen wasu munanan aikin bale wannan da ake shirin aikatawa watau kashe ASADEEK Kuka take yi kamar zata mutu Asaraki kuwa tamkar gawa kasa kawai yake kallo yan auna duniyar da abin cikinta yana mamakin da bata da tabas? Yaya zata ringa jan shi zuuuuu lokaci daya ta baro shi a cikin sahara tsaka tsakiya ga zafin rana ga rashin rakumi ga rashin ruwa ba tufafi bale takalmi? Sai rayuwarsa ta jagaliya ta ringa dawo masa, har zuwansa saman karagar mulki Hakane dama, idan kace ci da karfi zaka yiwa rayuwa zaka sha kallo gannin idannuwanka...... A kausashe MAI DAMAGARAM ya fadi nasu sakamako ta hanyar tsare su da tsatsaruran kallo ya ce" *NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° ```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.``` °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *https://www.facebook.com/106494781436168/* 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 *OUMOUGHLOUK ITIBEL* _(ZAKIN SARAKAI)_ 🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻🤴🏻 _FREE BOOK_ *Na* *SAJIDA NIGER* 7️⃣0️⃣ A kausashe mai Damagaram ya fadi nasu sakamako ta hanyar tsare su da kakausan kallo ya ce" Kisa ta hanyar rataya a gidan duhu ne ya hau kanka Asaraki!, Matarka kuwa gidan kaso na shekara goma sha bakwai da horo mai tsanani da kuma tara ta makudan kudi dan ya zamo ishara a gareta da dukkan mai hali irinta!" Tabas waje banda kabara da hawaye da rikicin matasa kan su a basu macutan Aban datawa su yi masu gunduwa gunduwa babu abinda yake tashi A hankali ASADEEK ya saki sandar nan, sannan ya shiga warware rawanin dake kansa, wanda hakan ya saka kowa hankalinsa tashi Me yake nufi da warware rawanin kansa? Ba dai sarauta zai ajiye ba? Hakan ya sa kowa yin dif yana kallonsa har ya karasa warwarewa sannan ya sauke rawanin gaba daya saman wuyansa yana kallon mai Damagaram da jajayan idannuwansa a hankali ya ce" Na tuba aboki, a kai Tuzuruwar kauye gida kar ta summa, yaron ciki ne da ita kar na shiga uku na rasa wajen hutu............" Kasa kasa ya fadi abin, sosai kasa kasa, mai Damagaram din ne kawai ya iya ji, hakan ya saka shi sakin murmushi hawaye na zuba a gurbin idannuwansa kamar yadda ASADEEK shima nasa idannuwan ke zubar da hawayen A hankali mai Damagaram ya ce" Alhamdulilah, Allah kennan, mai kawo sauki cikin zafi, Allah ya buda ido lafiya.........." Sannan ya kalli wajen Sheikh a tausashe ya bada damar a je a mayar da su gida su dukansu, dannan dukkan wanda ba zai iya kallo ba ya tafi an bashi dama A zabure ASADEEK ya juyo sanadiyar jin tsinkewa da mari mai karfi da fasa ihun muryar mace ya zuba masu ido, BAHIJA ce ta dankaro da gudun balaki, sai dai bata idasa zuwa jikinsa ba yaronsa ya dauketa da gigitacen mari dan ya farkar da ita daga mafarkin da take na son rungumar UMUGHLUK ITIBEL, hakan ya saka ta saka tartsatsin kara ta zube a kasa, a haukace muryarta na rawa ta ce" DAMA KAINE UMUGHLUK ITIBEL?, KAINE WANDA IYAYENA SUK CE ZASU AURA MIN NA KIYA NA CE NI AKOY WANDA NAKE SO, ASHE KAINE WANDA BAKE HAUKA IDO RUFE? KAINE WANDA NAKE JI KAMAR ZAN MUTU IDAN BAN AUREKA BA? KANA SANE KA KYALE NI NSKE HAUKA? TO AMA NI MENENE LAIFINA? INA CE KA SAN CEWA NA BIJIRE MASU SABODA KAI, KAINE KA ZO GIDANA KACE KA ZO SABODA NI, DAN ALLAH KA DUBE NI, BANI DA RUWA BALE TSAKI A SHIRYE SHIRYEN SU, BAN SANI BA, BABU RUWANA, NI DAI NA SAN INA SONKA, KODA MATA HUDU NE DA KAI KA SAKI DAYA KA AURENI, BALE SU BIYU NE BABU RUWANA DA WANI LAIFINSU, NI KAI NAKE SO ZAN KUMA RAYU DA KAI, DAN ALLAH KA TAIMAKENI KA AURENI IDAN BA HAKA BA ZAN IYA MUTUWA" Turus suka yi, su biyu da ake neman rakawa, suka juyo sunna kallon ikon Allah da kuma shi din dake tsaye yana kallonta HUZNAH ta sake kallonsa da kyau, kasa kasa ta ce" NADIRAH, kar fa zuciyar tausayin mijinki ta hayo shi yanzu, ina mai tabatar maki yana iya auro wancen ya kawo mana mu shiga uku, ke kin ga alamun zata barmu a dakunnanmu kuwa?" Nadirah dake ta shashekar kuka ta yi tsuru tsuru, kasa kasa ta ce" Me zai hanna ya zo mu je ya yi barci? Ni fa du ganni nake yana iya summa, in ba haka ba babu inda zamu je, kin san Asadeek zai iya aurotan kuwa? Wace ta bijirewa iyayenta saboda shi tsaf zata ci mana uwa Aunty" Ikon Allah Jakadiya ta tsaya kallo dariya na cinta, Auta kuwa kawai dolema ta saka yar dariya tana rungume hannayenta tana kallon tsayuwar da suka yi suka harde hannaye Sheikh shima dariya ya yi yana girgiza kai, ya bada umarnin a tafi da ita gidan baki, a bata dama t dawo hayacinta sannan ta koma gidansu na familly , domin sarauta ta sauka daga kansu tuni, an dora ainahin dan sarkin mai adalci, jinnin sarauta mai mutunci, da kyar aka cicibeta tana dirari tana ihu tana waigo shi aka fitar da ita, shi kuwa ya sauke ajiyar zuciya yana dawowa wajen mai Damagaram a zuciyarsa ya dauki niyar in sha Allah zai taimaka mata, zai saka a sakata a hanyar da idan ta yiwa kanta adalci zata ji dadin rayuwa ta tubarwa Allah, in kuwa ta ki shikenan, shi dai yanzu kuma gaskiya matan cen biyu da suka juya bayan an tafi da ita baya tunanin zasu bari ya karro wata, to tuzuruwar kauye har ba zata ce a rabu bs? Ta aika tace a rabu ya shiga uku Sai da komai ya tafi yadda ake so sannan baki kowa ya kama gabansa, matasa kuwa sai da ya yi magana da babar murya cewa babu su babu tarda ahalin asaraki, su barsu su rayu yadfa suke so, du wanda fa ya tada doka koda da sunnansa ne sai doka ta taka shi!, Da wannan ya shige gidansa, bangarensa ya tarda matan rayuwarsa, su uku an yi girki na gani na fada abin mamaki ana zaune ana hira harda wasa da dariya Yana zama ya saka su a gaba HUZNAH ta duka har kasa tana hawaye ta nemi gafararsa , sosai ya ji dadin haka harma ya saka masu albarka baki daya sannan ya umarci auta maza ta tashi mijinta na jira Mikewa NADIRAH ta yi tana murmushi ta kama hannun Auta ta ce" Allah ya bamu alkhairi Y'ar gidan momy mu je" Da mamaki yake kallonta, hakama HUZNAH wace jikinta ya karra yin sanyi A yanzu ta sani NADIRAH na son ASADEEK tamkar ranta, ama ta fita hankali da wayo ta juya kai ta tafi ta barta a gabansa , lalle zata yiwa kanta karatun ta nutsu kar ta barar da kimarta a idannuwan mijinsu ta hanyar yin koyi da dane zuciyarta a kan kishinsa ta gabatar da kishi tsaftatace ko dan ta karra samun fada a zuciyarsa Yana kallonsu har suka shigewa ganninsa, sannan ya sauke ajiyar zuciya, bai zaci haka ba, kuma a cen kasan zuciyarsa ya so ya kwana da ita a kirjinsa harma ya ji dumin babynsa, sai dai wannanma dake gabansa matarsa ce kuma mai kaunarsa ce, da wannan ya bata dukkan kulawar da ta dace, itama ta bashi, har aka wayi gari yau HUZNAH ta kawo daki, itama ta zo a mace, Asadeek ya san wacece ita, ta kuma ji menene mazan da take mararin ji har tsoron hakan da neman agajin a barta ta huta ya damketa, dan kuwa ta samu maza a lokacin da suka sake sannin ciwon kansu suka iya haukata mata ta yadda sai sun ji kamar zasu sume dan rikicewa da dadadan lamari kuma zazafa wa bakon shiga........................ Kwonci tashi Asarar mai rai Yau ya kama wata takwas da aka yankewa mazaluntan wannan ahali hukunci, ya kuma kama watan haihuwat NADIRAH wace ke rainon cikinta cikin kula da tatali na jama'ar dake zagaye da ita, tamkar zasu cinyeta , bama da cikinta ya kai wata bakwai ya zamana idan ta motsa sai dai dan ta yi tafia dan samun lafiyar jikinta da ta abinda yake cikinta, domin gogan ya gama tsare gaba, ya tsare baya, yace aa baya son garaje a bi a hankali zai fi alkhairi, idan ka ga yana garaje yar mutane ya tura saman gado, a nan fa zai ce ne hanya yake so ta budu da kyau dan abinda ke cikinta ya samu fitowa lamun lafiya, ita fai bata da abin cewa sai dai ta jure ta rintse ido, dan kuwa ASADEEK ba abin ya yi ya gama tana barci bane, dole sai ta dadage kar mata da girmansu su ringa ihun a taimake su Innarta, tunda cikinta ya tsufa ta sake dawowa bangarenta, dan kuwa Habu yakan turota fa kansa ne dan a yanzu sunne manya manyan masu algaitar fadar UMUGHLUK ITIBEL elhazai ne, ganninsu sai da takarda........., Tana nan ta dafa wannan ta bata, ta dafa wancen ta bata dan a samu saukin haihuwa ga ruwan rubutu ba dare ba rana daga aban birni, inda innar birni ke nata rokon ALLAHn ta hanyar hanna kanta barci tana rokon Allah ya raba lafiya ....................................................... Nishi take yi da dukkan karfinta, a cikin dakinta na barci ne, zufa take tsiyaya kamar babu sanyin ACn da HUZNAH ta kure ta basu waje, ama kan dan ya ki fitowa Innarta dake tsaye tana matsar hawaye hannunta rike da carbi fadi take" Indi, kamar zaki yi kashi haka zaki nisa, ki yiwa Allah ki yiwa annabi ki nisa dan nan ko y'ar nan su fito hankalinmu ya kwonta, nisa mana" Ina, Nadirah ba baka sai kunne, idannuwa kawai take zarrowa tamkar zata ciro su ta yarr, azabar ta kai wajen da ba zata iya magana ba yau sai dai nishin da kuma amshi hailalar da Matar Sheikh ke maimaita mata a tausashe tana faman fada mata an kusa ga kai nan ya bado fitowarsa ne dai bai fito ba Lalle a yau ta yarda cewa idan Kanta da na ASADEEK za'a hada a yi na danta ta shiga uku, jama'a babu wanda nasa kan ba zai amshe langa uku ba tsaf , ina ga shida? Ita kam tata a nan zata kare kuma, shikenan sai dai a ringa fadin ai an yi wata NADIRAH a zamanin da ya shude A waje kuwa, fifitu HUZNAH ke yi masa, yana zaune hannayensa bibiyu a dafe da kummatunsa ya zubawa SHEIK ido, wanda a dole ya janyo shi ya sako shi dakin nan dan da ya kawo matarsa hannunsa ya riko yace idan baka zo ba in na summa wa zai dauke ni? Gashi dai tun dazu ya yi wani tsuru tsuru yana kallonsa sai kuma ya kalli dakin, sai ya sake kallonsa ga zufa sai sjika maza take kamar shi ke nakudar yana ta yarfe hannu, ita kuma HUZNAH na famar masa fifitu da hannayenta kamar ta haukace dai itama bayan ga AC na kada su A tausashe Sheikh ya ce" Ka yi addu'a mana ASADEEK, ka san dai ba za'a kaita asibiti ba ko? Ka sani sarai" Da hannunsa ya nuna cewar yana yi a zuciyarsa sannan ya sake cira kai ya kalli dakin, kai innalilahi wa inna ilaihi rajune, haka haihuwar da take? Kalau fa suka zagaya da ita jiya da yaman nan, ama da asusuba ace masa wai tana gwuiwa? Gasu a gwuiwar har wata asubar zata zo shiru? Lalle a gaishe da mata, wannan ko kashi makayi ne ya rike ka ka kasa fitarwa na awa daya sai ka ji kamar zaka summa bale kan dan mutun? Ga tuzuruwar kauye da katon kai, shi hanyar cema gaba dayanta in yana aunawa sai ya ji gwara dai a je asibitin nan, in ba ikon Allah ba yaya za'a yi hanyar dake komawa ta matse taf kan Da ya fito? An sha daga, kafin kai yake fitowa, cikin hikima ta idasa zaro jikin wanda ke tafe da uwa, Yaro ni kosashe jajajir da shi masha Allah ga ni'imat gashi luflufluf a lulube a saman kansa, hannayensa a jimke, ana kuma ciro shi ya calara kukan da ya saka ASADEEK mikewa a haukace yana zarro idannuwansa, sai da SHEIK ya riko shi domin dakin ya nufa da nufin shiga bayan ba zasu so ya shigar masu a irin wannan lokacin da haihuwa ke raunata mata ba Tarin farin ciki sai da ya saka su zubar da hawaye, cikin sauri Inna ta shiga kimtsa shi yana cacalara kuka kamar zai tsage dakin tana aukin yi masa waka tana juya shi kadan kadan har ta saka masa sutura tana kallo matar SHEIK ta kama NADIRAH ta shige da ita bayi a hankali bayan ta dauke ledar haihuwar ta yi ciki da ita , ita kuma ta nado jaririn dake ta yanyar yanyar ta fito da shi fuskar nan tata kamar ginar auduga ta miko shi wa HUZNAH tana fadin" Wannan miji nawa dai toh, ba dole ya ta ringa zarar ido kamar ta ga mala'ikan mutuwa ba, gayanan yatsa a baki ko me yake nufi kuma? Gaskiya ya kama kansa dan yata barcima zata yi...." ASADEEK hannunsa na rawa yana kallon jaririn bayan an dora masa shi a hannayensa sai ga Auta ta shigo da gudu dan kuwa tunda abu ya kankama HUZNAH ta sanar mata , ita kuma tace ina ai ba zama sai AGADAZ, sai gata ta shigo ta ci karro da farin ganni Fadin murna da farin cikin wannan ahalima bata baki ne, kafin kace menene wannan gari ya dauka, murna ta cika ko'ina, hanadallah kawai ake yi, farin ciki kawai ake yi ba baba ba yaro, abu ne da ake jir ake nema ido rufe Sunna gama gyarata suka fito suka fice baban falonta aka bar ASADEEK shiga ciki da babyn a hannunsa A hankali ya haura saman gadon da aka cenza shinfida da sabon abin shinfida , dakin sai kanshin turaran ruwa na daki yake dan an zuba shi sosai an gyara ko'ina sai walwali yake karnin nan an dake shi da hypo an ci karfinsa da turaren wuta Ta yi laushi sosai tana rufe da bargo, idannuwanta kasa kasa take kallonsa har ya idasa hayowa ya rungume babyn a kirjinsa yana kallonta idannuwansa cike da launi na tsantsar soyayarta a cikinsu a hankali ya ce" Allah ya yi maki albarka, Allah ya raya *TUFAINAT*" Idannuwanta ta lumshe a hankali tana murmushi sannan ta jimke hannunsa a cikin nata , sunnan dda take fada masa tana so ya sakawa yaronta, itama ta ji dadin haka sosai a ranta A hankali ya saka yaron a tsakiyarsu ya zauna yana ta tofa masu addu'a har barci ya dauke uwar, sannan ya dauke dan ya je ya kaina Inna Hindu dake tsaye kan kaffafuwanta ta yi nan ta yi nan da waya a hannu fadi take itace Hindu ta habu uwar Indi matar UMUGHLUK, yau dai Indin ta haihu ga dan da nan masha Allah da shi a zo biki Tun daga ranar ya zamto babu hutu babu masala tsinke a fada har ranar sunna ta zagayo aka zanna sunna aka sha wunin biki cikin farin ciki da kwonciyar hankali Daga wannan lokaci lamari da yawa ya cenza, daraja da kima tata ta sake nin'ninkuwa a idannuwan mijinta da al'umar gari, sosai suke farantawa junna rai sunna kuma kare mutuncin junna da bacin ran junna A tsakaninta da uwar gidanta kuwa, mu'amala ce ta wayewa da kuma zama da zuciya daya Ba maganar ba sabawa dan kuwa rayuwa tsakanin harshe da hakorina akan sabawa bale mutun da mutun, sai dai du tsanani ana kokarin sako tsoron Allah da kuma kare hakkin makoci dan a ringa tafiyar da mu'amala lafiya Sannu a hankali ta zubda wanka, har ta koma bakin aiki, inda baby ya zamo fan yawo abinsa kulun yana bayan inna Hindu ko bangaren HUZNAH, wace a yanzu itama ake yi mata tsatsamin cikin dan kuwa wata ya shige bata ga al'adarta ba, ga kuma yan ciwuka dake sakota a gaba ............. A ranar da ta koma baban daki sai da ta ringa ihun ya kyaleta haka, dan kuwa sai da ya dauki fansar kyaleshi da ta yi na tsayin kwana arba'in wai ita wankan jego, hanyar nan sai da ta ji kamar zai dade mata fata , da kyar ya sarara mata yana lekenta zuciyarsa cike da wani irin mamakin halitarta, itace dai karama, ama kuma a lamarin nan ta dame HUZNAH ta shanye, sai dai ya bar abinsa a ransa burinsa a kulun kwananta ya zagayo ya labe tunda magariba sai sallar asubahi.....to yaya zai yi da ransa, tuzuruwar kauye da ta tashi shigowa rayuwarsa da tumtube ta shigo, tunda ta auko kuma ta kanainaye gurbin adalci kawai ta bari a zuciyarsa................. ____________ranar kai ziyara gidan yari____________ A nutse yake tafia, gefensa Inna Hindu ce cikin zumbulelen hijabinta tana goye da Yarima ko nace daga bayansa dan kuwa a zagaye suke da dogarai da kuma Sarkin yanka sunna ziyartar mutanen gidan yarin har suka zo dakin da Umma ke ciki Tun daga nesa kadan zaka ringa jin wani irin wari da duhu a daki har ka iso, sunna isowa da sauri ya dauke kansa, domin Umma a shanye take ta baza kafa kuda sai bin jikinta yake wanda ke fitar da wani irin ruwa mai tsami , haka kuma jikinta du ya yi wani irin kuraje luhu luhu, fatar jikinta ta dafe, gashin kanta tamkar na mai cancer du ya zube ya yi furu furu, ta rame sosai sai manyan idannuwa , ita daya ce a dakinta domin wa'inda suke daki daya sun gudu dan idan ciwo ya yi ciwo haka take yagar fatar jikinta tana ihu, an kaita asibitin ya fi a irga, ana bata maganin ama sai a hankali jiki fa ya tabu, wanda a yanzu take rokon a kasheta ta huta, abin ya gagara Juyawa ya yi yana umartar su koma, a lokacin da ta hangi Hindu ta kuma hango goyon dake bayanta, a lokacin ta saka wani kukan mage mage kare kare tana nuno bayan na Hindu, dan kuwa wani irin abu da ya ringa tukota kennan dai da gaske har haihuwa ASADEEK ya yi? Lalle ita ta zo a banza zata koma a banza.................... Asadeek kuwa, a tausashe yana dan kallon kasa da irin girmama ya ce da Inna" Mamah, a raka ku gida, zamu je kauye mu dawo" Inna ta amsa ta juya dogarai suka sakata a tsakiya tana taku daidaiya ana gaisheta tana amsawa hakoran nan a fili da hakoran makarta bibiyu sama da kasa suka wuce ciki A cikin mota sunna tafe Sheikh ya dube shi, a hankali ya ce" ABU TUFAINAT, murmushin me kake yi?" ASADEEK ya juyo ya kalli Sheik, ya yi murmushi ya ce" Ina yin dariyar sarkin yanka ne, yace wai anya zan kuma.iya yarda da wani dan Adam a kan abinda Umma ta min?" SHEIK na kallonsa ya ce" Nima na ji tsoron haka sosai" Asadeek ya koma ya ringesa, cike da iza ya ce" Idan na yi haka kennan ban godewa Allah ba, ai dole za'a iya haduwa da haka, ba kuma haka zai sa mutun ya rufe kansa ba, MUTUN ai rahama ne, Kamar yadda aka samu na banza sosai, haka kuma ake da na kirki sosai, misali GAKA nan, ina alfahari da hakan...ina kuma fatan mutuwa cikin jarabawa, dan kuwa bawan da Allah ke so yake jarabawa........" SHEIK na murmushi ya ce" Amen ya Allah " Nima na ce *ALHAMDULILAH* *ALHAMDULILAH* NAN NA KAWO KARSHEN LITAFINA MAI SUNNA UMUGHLUK ITIBEL, INA ROKON ALLAH YA YAFE MIN KURAKURAN CIKI, SANNAN INA ROKON DU WANDA NA BATAWA YA YAFE MIN, INA MIKA GAISUWATA A GAREKU BAKI DAYA, DAN KUNNA DA YAWA WALAHI KUMA KUNA DA MAHIMMANCI SOSAI A RAYUWANA......, INA KUMA FATAN ALLAH YA SA DAGA WANNA LITAFINA NA GABA IN AJIYE RUBUTU HAKANAN, MAI TAKEN *ƊAKIKA ƁIYAR* Nobel dina na gaba in sha Allah......... *ƊAKIKA ƁIYAR* TAKU CE yar mutan NIJAR......... *Sajida* Nd