👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) 𝗕𝗜𝗦𝗠𝗜𝗟𝗟𝗔𝗛𝗜𝗥 𝗥𝗔𝗛𝗠𝗔𝗡𝗜𝗥 𝗥𝗔𝗛𝗘𝗘𝗠 اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 Ina mai godiya ga Allah da ya bani iko da daman fara wannan sabon littafin nawa mai suna 'YAR KARUWA, Allah sa mu kammala lafiya, duk abinda ya ke ba dai-dai ba a ciki Allah ya yafemu duka, ni mai rubutawa da ku masu karatu, FAN'S ina matuƙar ƙamnarku, Uwar batoorl na mugun yinku irin sosai ɗin nan, masu daraja habibties.🥰 SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NA FARKO DA KU ZAN FARA KAMAN YANDA NA YI ALƘAWARI. Masoyiya Bealkysou Ummu Adeel tawan 🅿️ 1 _ 5 Matashiyar yarinya ce zuƙeƙiya fara, farinta dai-dai, 'yar kimanin shekaru 20 da haihuwa, durƙushe take akan guiwowinta ta yi kneel-down a gaban wata mata wacce ko ba'a faɗa ba kasan mahaifiyarta ce duba da kaman da suke yi da kuma maganganun da matashiyar budurwan ke yi. Cikin tsananin kuka mai nuni da stagwaran taƙaici da kuma tsaban damuwan da take ke ciki ta ce, "Haba Mami na, Mami dan Allah dan Annabi ba dan ni ba, kuma ba dan halina ba ki bar wannan rayuwa, Mami kina zubar da mutuncin kanki kina zubar da na 'yar ki, Mami da girmanki kina rayuwa irin ta yara ƙanana marassa tunani ko mafaɗi, Mami ke fa ya kamata ki stawatar mini idan kinga ina ƙoƙarin sanya kai na a irin wannan lalatacciyar rayuwan, amma fa Mami ke da kanki kike yi ba ma ni ɗin ba, haba Mami na ina iliminki da tunaninki kika zaɓa mana wannan rayuwa irin ta jahilai...." Maganan dake baki na ne ya maƙale a maƙoshi na, sakamakon wani azababben marin da Mami na ta kifa mini, miƙewa tayi tsaye tana huci ranta a ɓace kaman ko da yaushe idan hakan ya faru tsakaninmu, idanuwanta ta zuba mini tare da cewa, "BANAFSHA har rashin kunyar ki da fistaranki sun kai haka? Ina mahaifiyarki kina sokamun baƙaƙen magana, ni kike faɗawa ina rayuwa irin ta jahilai? Ni kike ƙira jahila Banafsha? Irin tarbiyyan da na miki kenan ki nunawa duniya ni ma kin renani balle wasu? Banafsha ni kike faɗa wa haka?" Mami ta ƙarishe maganan cikin stananin ɓacin ran da har idonta na ƙoƙarin sauya kala. Cikin kukan da ya zamo mini jiki dan in da sabo na saba, sai na ce, "Allah ya huci zuciyanki Mami na, amma wuyana bai yi ƙwarin da zai sa nayi suɓutan harshe a kan mahaifiya ta ba, koma menene ke ɗin uwa ce a gare ni kuma ko ya kike ke mahaifiyata ce, amma ina mai haɗa ki da Allah da Manzon sa Mami kiji tausayin rayuwata kibar wannan lalatacciyar rayuwan, munanan maganganun da mutane ke jifa na da shi tun baya damuna har ya fara mini ciwo, Mamina dan Allah kiji tausayin maraici na ki daina wannan rayuwan ko dan ni Mami, wallahi duk inda naje suna ɗaya ake qira na da shi manya da yara, duk inda na wuce sai ace ga 'YAR KARUWA! Mami tun ana faɗa a ɓoye har takai mutum zai staya a gabana ya ce mini hakan kuma ba ni da yacce zan yi, dan girman Allah Mami kiji tausayi na kibar wannan rayuwa mai cike da kunyan duniya da lahira, Mami ki tuna fa akwai mutuwa fa, kuma ba mu san yaushe, a ina, a wanne hali, ta yaya za ta riske mu ba, dan Allah Mamina ki daina kinji" na ƙarishe maganana cikin sigan tausayi ina share hawaye mai ɗumin gaske da ke bin kunci na. Mamina zama tayi ta dubeni tare da cewa, "Maganar da nake faɗa miki a kullum ita ce zan ci-gaba da faɗa miki Banafsha, ni ba karuwanci nake yi ba sana'a nake yi, wanda kuma da wannan sana'a na siya gida na kai ki makaranta, cinki, shanki, suturanki, maganinki, da komai naki har kika kawo i zuwa yanzu da kuɗin sana'ar nan nake miki, me yasa kema za ki bi ta faɗin jama'a ba za ki fahimci mahaifiyarki ba? In na zauna bana komai kina ga akwai mai kula da mu? Akwai mai ɗaukan nauyin karantunki, cinki ko shanki ko suturanki? Ko da ace aikatau muka je gidan mutane to tabbas nasan za'a nemi lalata mini ke ko wulaƙanta mu, wanda ni kuma ba zan jure hakan ba, akan abu ya same ki gwanda ko duniya ne su taru a kaina su ce komai ma sannan sunan da ake ce miki 'YAR KARUWA ya bar damunki in baki fahimci mahaifiyarki ba babu mai fahimtarta Banafsha, ki dubi rayuwan yanzu da idon basira da kyau, ko bara na ce zan yi dan na kula da ke to fa tabbas za'a nemi lalata miki rayuwa ko kuma ni ɗin, Banafsha duk da ke yarinya ce, amma a wannan shekarun naki ya kamata ki fahimci rayuwa da kyau." Kallon Mamina nayi da idanuwana da kullum cikin zubar hawaye suke na ce, "Wallahil Azeem Mami na gwammaci muyi rayuwan aikatau akan irin wannan rayuwa, na kuma zaɓi muyi rayuwan bara akan wannan rayuwa, Mamina gwanda na zama 'yar talla mu yi sana'anmu ko na rufawa kai asiri ne ya fi mini akan wannan rayuwan, sannan lalata rayuwata ba wanda yake da ikon hakan in har Allah bai ƙaddara hakan ba to babu wanda ya isa tunda kina min addu'a, kuma Allah zai kare ni dan addu'an bakin mahaifiya ba a maida shi, dan Allah Mamina ki daina, wallahi Mami akwai mutane na gari da yawa a rayuwa masu yi dan Allah ba tare da zalunci ba, nifa Mami ko baran kika turani zanyi na nemo mana abinda za muci karatu ko wani sutura na haƙura da su, mutuncinki da nawa su ne abun da nafi buƙata, wannan suna da ake faɗa mini yana sa zuciyata tana mini zafi sosai-sosai Mamina, dan Allah inma ba za mu yi wani aikin ba mubar garin nan mu koma wajan 'yan uwanki ko na mahaifi na ne kinji.....", wannan karon ba mari ne ya maƙalar da sauran maganan dake baki na ba domin kuwa Mamina rufe ni tayi da duka ko ta ina kaman an aiko ta, da ƙyar aka shigo aka karɓe ni. Maman ƙawata Umaima ce ta shigo ta karɓe ni ta riƙe hannuna muka tafi gidanta wanda ya ke gidan su babbar ƙawata kuma Aminiyata wacce banda kamarta. Matar da ta shigo ta karɓeni wacce muke ƙira da Ummu, kallona tayi ta ce "BANAFSHA wai me yasa kike son yawan yin sa'insa da Maminki ne da har yake kai da ga miki irin wannan dukan ne? Yanzu ba dan Allah yayi fitowa na ba kin san halinta za ta iya miki rauni, Banafsha kin girma fa yanzu ba da bane kin zama budurwa duka bai kama ce ki ba kiwa mahaifiyarki biyayya ki kuma yi haƙuri komai zai wuce kiyi ta addu'a." Cikin tsananin kuka da ciwon da jikina ke mun na dukan da Mamina ta mini ina sheshsheqa da muryana da ta fara dishewa na ce, "Um..mu yaa..yaa.. yaya zan.. yi? Ummu, Maa..mi na, Ummu me yasa sai ni? Wan.....nann ra..yuwa..n akwai...ciwo mahaifiyar mutum ta dinga kule-kulen mazaje daban-daban, Ummu kiji fa sunan da ake qira na da shi a anguwan nan 'YAR KARUWA! Ummu hakan akwai daɗi? Ummu ya zanyi da rayuwa ta? Ya ake so nayi? ina ake son na saka kai na? Ko sai na mutu kowa hankalinsa zai kwanta?" Na faɗa ina ƙara fashewa da mastanancin kukan da zuwa yanzu sautin ma ba ya fita. Ummu kallona tayi cikin sigan rarràshi ta ce, "komai na duniya mai wucewa ne Banafsha, ke dai ki ci-gaba da addu'an Allah ya kawo miki miji na gari kiyi aurenki wanda nake fata zuwa wannan lokacin Allah yasa komai ya wuce." Cikin kuka na ce, "Ummu wa zai yi aure? Wa zai aure ni? Ina 'YAR KARUWA wa zai auri yarinyar da uwarta ke lalatacciyar rayuwa? A'a Ummu karki faɗa min abinda ni da kai na nasan ba zai taɓa faruwa ba, kuma nima ba zan yaudari kai na ba, nasani ni da aure har na mutu sai dai a lahira idan ana yi, zan zauna da Mamina na dinga addu'an Allah gyara mana rayuwanmu ya shirya min uwata, amma ba zan taɓa yin aure ba dan nasan ba mai aure na, kuma ko an aure ni za'a goranta mini." Ummu murmushi tayi wanda hakan ya ɗan sauƙaƙa mini abinda ke damuna a zuciyata, dan sosai nake jin Ummu a rai tamkar mahaifiya ta, Ummu ta ce, "Banafsha ki rubuta ki ajiye ni Ummul-khultum na ce za kiyi aure in Allah ya yarda, kuma aure ne irin wanda ba ko wacce yarinya ke dacen yi ba sai wacce Allah ya ƙaddarawa hakan, za kiyi aure in Allah ya yarda wanda mijinki na tabbata zai sanya ki mance kin ma taɓa shiga wannan halin quncin rayuwa, duk bawan da ƙaddara ta stananta a rayuwarsa to tabbas gaba kaɗan idan da rayuwa zai riske alkairi mara misaltuwa, to ina so kema ki ɗauka hakan, duk da akan jarabawan rayuwa da wani ke ciki to naki ba komai bane, kuma bawan da Allah ke jarraba shi Allah ke so, kibar wannan tunanin in Allah ya yarda za ki yi aure." Kallon Ummu nayi idanuwana har yanzun da burbushin ƙwalla na ce, "Ummu nasan da haka, amma babu mai aure na ina 'YAR KARUWA! sannan ko da nayi auren to Ummu tabbas wulaƙantaccen rayuwa zan yi dan kuwa zan zama tamkar mujiya ko saniyar ware yacce ake nuni dani yanzu haka can ma za'a yi, za'a dinga gorantamini a ce ni Ƴar karuwa ce a dinga wulaƙantani, Ummu ni ko kaɗan ma bana ƙaunar maza, Ummu na tsani maza gani nake kowa irin halin sa kenan bin mata." Cigaba da rarrashina Ummu tayi har Ƙawata Umaima ta shigo ta same mu a haka, ganina kawai da tayi ta fahimci me ke faruwa dan ta sani tabbas labarin gizo baya wuce na ƙoƙi, dan kusan aikin kenan kullum ni da Mamina, idan ba'a yi da safe ba za'a yi da yamma. Cikin yanayi na rarràshi ta ƙira sunana ta ce, "Masoyiya Banafshaty." Jin sunan da ta qira ni da shi sai da na ɗan murmusa dan kuwa Allah ya gani ni da Umaima ba ƙaramin ƙaunar junan mu muke ba, duk irin halayyan mahaifiyata da yacce ake yama-ɗiɗi da ni a gari hakan bai dame ta ba ko kaɗan dan Allah take ƙaunata nima dan Allah nake ƙaunarta, duk gidansu suna ƙaunata illa iyaka yayansu ɗaya da ko giftawa nayi sai yaja staki in kuma ya ganni da Umaima to ranan sai tasha na jaki idan dai ba wai Ummu na gida bane ta gani ta hanasa, gaba ɗaya ya staneni shi da mahaifiyarsa, ba iya su ba kowa a anguwar kallona yake da laifin mahaifiyata kowa ɗauramun laifin da ban taɓa kusantan shi ba yake yi, in ka cire wannan gida to ba gidan da nake shiga a anguwan mu, kuma bayan Umaima ba ni da wata ƙawa ko a makaranta. Cikin sigan wasa na harari Umaima na ce "Ba wata Masoyiya atou kar ki yaudare ni, kin tashi kin kama hanya kin tafi aiken Ummu ke kaɗai wato salon asa miki albarkan ke kaɗai ba, irin ba amanan nan, shi ne za ki wani ce mini masoyiya to na ƙi", na juya ga Ummu nace "Ummuna ai dai tare za ki raba mana albarkan ko?" Ummu na murmushi ta ce, "Dai-dai wa dai-da ma kuwa Banafsha 'yar Ummu." Murmushi nayi, ƙawata Umaima ta riƙe hannuna ta jani har cikin ɗakin su ta zaunar da ni a bakin gado ta ta ce, "Wai yanzu ke ni za ki cewa yaudara amma dai kinsan ƙaunar da nake miki na amanane ko?" Kukan da nake dannewa ne ya samu nasaran kuɓucemun, sai kawai na rungume Umaima ina kuka mai cin zuciya. Hankalinta ya tashi ita ma a take idanuwanta suka kawo ruwa sai hawaye kuma, bubbuga bayana take yi cikin sigan rarrashi ta ke cewa "Kiyi haƙuri haka dan Allah masoyiya, kukan da kike yi yana yawa ko so kike hawayenki ya ƙare ne? dan Allah kibar kukan nan bana so please Banafshaty." Cikin kukan na ce, "Umaima ya zan yi da rayuwa ta? Ya ake so nayi ne? Ni ji nake mutuwa ma tafi mini wannan ƙazantaccen rayuwan, dan Allah ace uwarka ta rasa abun yi sai karuwanci kuma a haka Mami ke cewa sana'a ce wai dama karuwanci sana'a ne? Mami ta ce bata so aci mutunci na ko a lalata mini tarbiya shi ya hanata zama haka ta kama wannan sana'a dan Allah wannan shi ne soyayya Umaima? Ta kwaɓar da mutuncinta sannan ta kwaɓar da nawa, shi fa mutunci Madara ne, a abinda Mamina ke yi wa zai ganta da mutunci idan ba ni da ya zamo mini dole ba?" duk cikin mastanancin kuka nake wannan magana wanda i zuwa yanzu kai na mugun sara mini yake yi kaman na cire kan na huta. Umaima ta ce "Banafshaty dan Allah ki yi haƙuri haka nan, ni dai mu ci gaba da addu'a komai zai wuce kin ji, kuma Mami na sonki fiye da yanda take faɗa ma dan Allah kiyi haƙuri kina addu'a kina kau da kai kinji" ta faɗa tana sharemun hawayena. Lumshe ido nayi nace "Umaima in dai wannan ce soyayya to tirr! da soyayya, Allah wadaran soyayya, bana son soyayya, bana ƙaunar soyayya, na tsani soyayyan, Umaima ko na kau da kai kan baya kauduwa domin muddin ina gida wani zai zo wajanta to sai naji zuciyata na tafarfasa zuciya ta kaman ana wastamun ruwan zafi zuciyata kaman ana ƙonemun ita, ji nake kaman na kashe kaina na huta, wallahi ba dan kisan kai zunubi ne babba ba da na jima da kashe kai na dan da wannan rayuwa gwanda na mutu na huta, Umaima imagine wai har YA DANISH shiima zai ce mun 'YAR KARUWA, stana da cin mutuncin ya wuce mutanen waje ya koma har kan mutanen gida suna min wannan wacce iriyar rayuwa ce?" Fashewa nayi da kuka mai ciwo tuno abinda ya faru ɗazu sai na ce, "Umaima kinsan me ya faru ɗazu?" Girgiza kai tayi tana hawaye dan maganan ya Danish ya mata ciwo ita ma sai ta ce, "Banafshaty kar ma ki faɗa min me ya faru kinji, yacce kike shanyewa ki shanye kawai, saboda ciki ba dan tuwo kawai aka yi sa ba ki yi haƙuri za ki ga riban haƙurin da muke cewa kiyi kullum da yardan Allah, babu jimawa za ki ga sakamakon Ubangiji akan jarabtar da ya miki." Hannunta na riƙo ina hawaye na ce "A'a Umaima, ko kaɗan wani abun ba zai riƙu a ciki ba dan riƙuwan sa tabbas masifa ne, haɗiye wani abun to barazana ce ga lafiyan mutum, kaman kai ne ka samu guba ka cusa a cikinka kuma ka ƙi zuwa asibiti a baka taimako, Umaima idan ban faɗa miki ba bazan ji sanyi a rai na ba wallahi ba abinda zan ɓoye miki a rayuwata indai bai kauce sirrin da Allah ya ce ya zama sirri na ba, wanda wannan nasan babu shi a kai na nikam, Umaima wai ɗazu fa ina kwance a ɗaki na ina bita haddan da ya rage mana kawai naga mutum ya faɗo mini ɗaki daga shi sai ɗan gajeren wando, wai yana tambaya ta ina Mami na ta tafi a hannu yake sauri yake" kuka nake sosai nace "Umaima kiji fa wai har ni ya ke gayawa wannan magana, to wallahi idan ita Uwata na haƙura ban ɗau mataki ba dan Uwata ce to su na kusa fara ɗaukan mataki a kansu in ta kama in kashe mutum in yaso nima a kashe ni, yaro ya zo babba ya zo dattijo ya zo stoho ya zo, Mami har da wanda ta kusa haifa take kulawa wannan wacce rayuwa ce? Haka da safe wani saurayi ya fito ɗakinta ina stugunne ina aiki kawai naji an zame mini ɗan-kwali ɗan iska wai gashina na burgesa irin na mamata", kuka nake sosai idan na tuna wasu abubuwan. Ƙawata Umaima rarràshi na ta ci-gaba da yi kawai dan ita ma abun sosai yake damun ta, ba ɓata lokaci zazzaɓi ya rufe ni ruf-ruf nan take na fara tari wanda nake ji tamkar zuciyata zan amayo dan azaban da nake ji a ƙirji na, hawaye nake ina tarin, wanda hakan ya storita Umaima, cikin ruɗewa ta fice ta ƙira Ummu suka shigo tare, Ummu ma ta ruɗe amma duk da haka ta mini faɗa na daina saka damuwa a rai na, sai da ta gyara mini kwanciyana ta lulluɓe ni sannan ta fice dan ta ɗauko mini magani, Umaima kuma tana zaune a gefe na tana aikin jero mini sannu tana hawaye. Ganin tarin yaƙi stayawa sai Umaima ta dube ni cikin tsananin kuka ta ce, "Banafshaty wallahi idan kika ja abu ya same ki ba zan taɓa yafe miki ba" tana gama faɗa kawai ta fashe da kuka mai nuni da tausayina da take ji, ta rungumeni nima kukan nake jikina sai rawa yake yi ga kuma ya ɗau wani azababben zafi kaman garwashi. Wannan littafi FREE BOOK ne in Allah ya yarda, dan Allah fan's ku nunamin soyayya kaman ko yaushe, sharhinku shi ne ƙwarin guiwa na, bana son tnx Sharhi nake so, ban yi niyan yin sa a paid ba kuma bana so ya koma paid, love U all My fan's ♥️ *** INA KUKE MASU SANA'A, SANA'A MAGANIN TAQAICIN RAYUWA. SAUQI YAZO MUKU HAR INDA KUKE DOMIN WANNAN BA IRIN NA SAURAN BANE Ga mai buqata a tallata masa hajar sa ko kuwa dai sana'ar sa to yai maza ya garzayo ga uwar batoorl mai tallata haja a rahusa mai sauqi domin kuwa har da alakoro ina yi. KU TUNTUƁE NI A WANNAN LAYIN NAWA 09161720046 WHATSAPP TELEGRAM Ko 07015870735 WhatsApp and call Ko Gmail nawa yarmalam96@gmail.com Akan rahusa mai sauqin gaske, sai kunzooooooo🤝 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Ƙanwa eclemah (Amarya) Fatan ayi biki lafiya a gama lafiya, Allah ba da zaman lafiya, ya sa ɗakinki ne har mutuwa, congratulations. My Heartbeat (ukhtynh) 2 month's Anvsy. Allah ya ƙaro zaman lafiya da ƙaunar juna ke da sweet babynki, Allah ya raba lafiya 🤣 اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 6 _ 10 A Haka Ummu ta shigo ta same mu muna ta aikin kuka, Umaima nayi nima ina yi kuma har yanzu ina fama da tarin da kuma zafin jikin, Ummu ganin haka rai ɓace ta rufe Umaima da faɗa sannan ta ɗaga ni ta bani magani, da ƙyar na haɗiye maganin kaman zan amayo da 'yan hanji na, Ummu koran Umaima a ɗakin tayi ta dinga shafa min kai na ba jimawa bacci yayi gaba da ni ina ta faman ajiyan zuciya, sai da nayi bacci sannan Ummu ta miƙe ta fice tana bina da addu'a. Umaima taya Ummu aiki ta yi har dai lokaci ya ja, na sha bacci na sosai duk da ba na daɗi ba ne, sai can yamma na farka, kuma a dai-dai lokacin Umaima ta shigo fes da ita dan har ta yi wanka, a kan ta na sauƙe idanuwa na da suka mini mugun nauyi, murmushi ta sakar mini tana tambayan ya jikin nawa, da kai na bata amsa na kuma mayar da idanuwana na lumshe su in ambaton Allah a zuciyana dan har yanzu ba wai naji abinda ke damuna ya tafi duka ba ne. Muna ɗaki Mamina ta shigo cikin gidan, a palour ta samu Ummu zaune tana waya, Ummu kaste ƙiran tayi ta tari Mami da murmushi suka gaisa, Ummu ko kaɗan bata cewa Mami komai akan abinda ya faru ba dan kuwa in da sabo to an saba da hakan tsakanina da Mamina. Mami ce ta numfasa tare da cewa, "Ummu ina yarinyar taki ta shiga?" Ummu na murmushi ta ce, "suna ɗaki da mutumiyar ta, da bacci take yi amma ina ji yanzu ta tashi dan na jiyo mostinsu." Da yake Mami ta kan shigo gidan sa'i da lokaci idan irin haka ta faru, kuma ta san ɗakin da nake zama idan na shigo, sai ta wuce ɗakin da muke, da sallama ta shigo, Umaima ce ta amsa da ƙarfi, amma ni ciki-ciki na amsa kuma ba tare da na buɗe idanuwana ba, Mami ganina a kwance bata kawo komai a ranta ba ta murmusa tare da ƙarasowa bakin gadon, sai da ta amsa gaisuwan da Umaima ke mata sannan ta ce, "boɗɗin Maminta taso mu tafi ko." A hankali na buɗe idanuwana da suka kumbura ga kuma hawaye kwance a cikinsu na zubawa Mamina su, ban ce komai ba kuma ban mosta ba dan bana jin zan iya tashuwa balle tafiya, Mamina tana kallon yanayi na ta shiga damuwa dan bata san banda lafiya ba ne, a rikice ta zauna bakin gadon ta taɓa jikina, da yake zuwa lokacin zazzaɓin ya sauƙa, to zafin jikin ba sosai ba, amma duk da haka da ɗumi, Mamina duk ta bi ta rikice, kaman za tayi kuka ta ce, "boɗɗi me ke damunki?" Nan ma shiru nayi ban ce komai ba, Mamina cikin damuwa ta ce, "Banafsha ki daina saka abu a ranki, ki saki ranki mamana, ki dinga taya ni da addu'a kawai dan wani abin nima ba da son raina nake yi ba, tashi muje gida kiyi wanka." Yanzunma dai ban ce komai ba sai ƙoƙarin miƙewa da nayi ina runste idanuwana dan har yanzu kai na yana mugun sara mini, amma tunda Mami ta ce mu tafi ba zan iya mata musu ba dan Allah ma ya gani ina ƙaunar mahaifiyata ina son mahaifiyata fiye da yacce nake son kai na, duk wani mafarki na da buri na ita ce ba wanda na sani sai ita ba wanda ido na ya taɓa gani da za'a nuna ace ɗan uwanane ko wani nawa sai ita, ita kaɗai gare ni shiyasa bana haɗa soyayyan da nake mata da na kowa. Miƙewa nayi amma ganin jiri na neman yasar da ni sai Mamina ta hau da ni bayanta kasancewar ba wani nauyi ne da ni ba duk da dai in ka ganni za ka ɗauka nafi shekaruna, ko na kai irin ishirin da ɗori hakannan. Fitowa muka yi a ɗakin ina bayan Mami na lafe abuna, Ummu ganin mu sai ta girgiza kai tare da yin murmushi ta ce "Yau kuma taɓaran Banafsha ya tashi, har goyo ya kai a mata, ah lallai ƴar gidan Mami jin daɗi ya zauna miki." Umaima tana murmushi ta ce "Nima Mami biyo ki zan yi a goya ni nima dan masoyiya ta fini nauyi ma." Mamina murmushi tayi wanda ako da yaushe yake zama makari sannan sirri na kyau da Allah ya mata, dan in ka kalli Mamina za ka ranste balarabiya ce ko bafulatana amma kuma duk ba abinda ya haɗa mu da yare biyun, bayan su Ummu sun gama zolayansu Mami ta fice da ni a bayanta tana murmushi muka yi gidanmu, kasancewan ba nisa tsakanin gidanmu da na su ƙawata Umaima. Jahar Adamawa a ƙaramar hukumar Mubi anguwan Kwaccam, nan ne anguwan mu, anguwa ne na masu saka ido da kuma damuwa da rayuwar da bata shafe su ba, mutane masu kiwon mutum ba dabba ba, komai aka yi idanuwansu na kai, ɗan madai-daicin gidanmu flat ne mai ɗauke da center palour sai kuma ɗakuna guda uku wanda ko wanne akwai banɗaki a ciki sannan daga gefe akwai kitchen, ba abinda Mamina bata saka mana ba na more rayuwa a gidan, dai-dai buƙatan talaka mai rufin asiri, wanda in ka samu irin sa dole ka ce Alhamdulillahi! dan kuwa wani ko kwatan-kwatansa nema yake bai samu ba, a filin gidan namu akwai kitchen a waje sannan da banɗaki, gidan bashi da wani faɗi sosai kuma ciki duka interlock ne. Har ɗakin da yake nawa Mami na ta kai ni ta kwantar da ni a kan madai-daicin gadona, juyawa tayi ta fice a ɗakin sai can ta dawo da abinci a plate da ruwa a cup da kuma magani. Ɗagani tayi ta zaunar da ni tana jero mini sannu ta ce, "FAƊIMAH tashi ki ci abinci ki samu kisha magani, kinji ko ƴar albarka ta Maminta." Miƙewa nayi na zauna tare da zuba wa Mami idanuwana, kallon mahaifiyata nake yi ina mai jin ƙaunanta na ƙaruwa a raina yana tsigar mini a ko wani sassa na zuciyata, ina jin ina ma muyi rayuwanmu mu biyunmu a haka ba tare da wasu sun shigo ciki ba, ina jin ina ma shikkenan Mamina ta daina wannan rayuwan, mu zauna haka abunmu ta kula da ni nima na kula da ita, amma sai dai kashh! nasan hakan ba mai yiwuwa bane, tana ƙaunata tana tausayina amma wannan rayuwa ya zamo ƙaddara a garemu ni da ita, kuma amsa sunan 'YAR KARUWA ƙaddara na ne, sai dai na yi haƙuri na karɓe sa da hannu bibbiyu. A baki take bani abincin ina ci kaman zan yi kuka, saboda a rayuwata ni bana ƙaunar cin abinci wanda ta wannan dalili ne har ulcer yayi nasaran mini mugun kamu, amma a haka Mami ta cigaba da bani har na kawar da kai na ƙoshi, sannan ta ɗau magani ta ɓare ta miƙo mini, nan fa gizo ke saƙar dan kuwa wannan ga'bar ita ce daru, nan na fara hawaye ina kuka ina girgiza kai banason sha. Kallona Mami tayi cikin lallashi da ta saba min a duk lokacin da zata ban magani ta ce, "Haba Sayyada Faɗimah shugabar mata, Nana Faɗimah, Fatima Bintu, batooler, Faɗimatu zahra'u, Sadiƙa, yarinyar kirki jaruma, da girmanki ai sai dai magani ya ji storonki, takwara ga ɗiyar ma'aiki SAW, yi haquri kibar kukan ki karɓa kinji zan baki abu mai daɗi." Ina kukan ina yarfe hannu na karɓa na sha, ajiyan zuciya na dinga jerowa kamun na koma na kwanta amma Mami ta tashe ni wai na wasta ruwa, langwaɓe kai nayi cikin shagwaɓa na ce, "Mami nikam ba zan iya ba sai anjima." Kallona tayi ta murmusa sannan ta ɗaga ni ta fara cire min kayan jiki na, tana gamawa ta ɗaura min towel tana cewa, "Yanzu Banafsha da girmanki kike so ki ce sai na miki wanka, kin fa zama budurwa yanzu, shekaru ishirin 20 ba wasa ba, ko in na aurar da ke haka zaki sa surki na sai ya dinga miki wanka kullum kaman bai da aikin yi?" Tura baki nayi idanuna har ya kawo ƙwalla dan maganan da tayi na ce, "Mami ni ki bari bana so, ba ruwana da maganan nan, kuma ba ruwa na da namiji balle aure." Mami ajiyan zuciya ta sauƙe kamun ta zauna tana kallona cikin yanayi na muhimmin magana za ta yi, sai ta ce, "Banafsha, na hane ki wannan magana, banda abinda ya ragemun a rayuwata a yanzu sai ganin na aurar da ke, domin kuwa aure shine mutunci ko wacce ɗiya mace kuma buri ga iyayenta suga sun miƙata gidan miji lafiya cikin mutunci, in Allah ya yarda mijin da zai auri Banafshan Mami sai ya kasance mai matuƙar sa'a, wanda ba shi da stara, in Allah ya yarda za ki rayu a gidan mijinki rayuwa ta matar Sarki." Wannan magana da Mamina tayi ba ƙaramin fama min ciwon dake zuciyata yayi ba, kuka ne ya ƙwace mun ba tare da nayi niyan kukan ba, cikin kukan na ce, "Mami ashe mutuncin ko wacce ɗiya mace aure ne? Mamina kinsan da hakan amma me yasa kika take sanin? Mami kema fa kina da iyayen amma me yasa ke ba zaki cika musu nasu burin ba ki riƙe mutuncinki, sannan kuma ki zauna a gidan miji, meyasa Mamina? Meyasa kika zaɓar mana wannan rayuwa? Why Mami?" Na ƙarishe maganan cikin matsanancin kuka mai cin rai." Miƙewa Mamina tayi ranta a matuƙar ɓace, wanda na tabbatar rashin lafiyan dake damu na shine kawai ya cece ni daga samun sadakan mari ko kuwa duka daga Mami, a fusace ta nuna ni da yasta cikin fushi da ɗaga murya ta ce, "Banafsha, kar ki yarda ki tunzura ni har ɓacin rai yasa na miki baki." Kallon Mamina nayi ina kan kuka na ce, "Mami wallahi ko kin stine mini ba zai taɓa kama ni ba har abada in dai akan wannan maganan ne, domin Allah ya faɗa ba ya kama bawansa da laifin da bai aikata ba, Allah ba azzalumi bane, sannan Allah ya sani gaskiya ce kuma Allah da kansa ya ce ko iyayenmu ke yin ba dai-dai ba mu faɗa musu gaskiya komin ɗacinta, dan Allah Mamina kiyi haƙuri gaskiya ce na faɗa, amma in har na ɓata miki rai to ki yafe ni, kada kiyi fushi da ni, Allah huci zuciyanki Mamina." "Tashi kije ki wasta ruwa kuma kina fitowa ki tabbatar kin yi sallah kamun ki kwanta" Mami na gama faɗan haka ta fice a ɗakin. Tashuwa nayi na shiga banɗaki ina cike da tunani dan zuwa wannan lokaci idanuwana sun kafe ba hawaye, kukan yau kuma ya tsaya sai kuma na gobe, dan wannan wani abu ne gare ni da kullum shine sana'a ta kuma ƙalubale na, ba ranar da gari zai waye har rana ya faɗi ban yi kuka akan halin Mamina ba ko wani abun idan ta mini. Ina gama wanka na ɗaura alwala sannan na fito, ko mai ban shafa ba balle wani abun, humran da Mami ke sayamun kawai na shafa a inda ya kamata na sassan jikina, sannan na buɗe drawern kayana na ciro simple material riga da wando da mayafin sa wanda ɗinkin ke kama da Pakistan-dress, ina saka wa na ɗau hijab na tada sallahn magrib, ina idarwa na ɗauki Qur'ani na fara karatu, nice ban tashi akan darduman ba har sai da nayi sallahn isha'i na tabbatar hadda na ya zauna, sannan na naɗe na ajiye sa, da hijab ɗin jikina na fito palourn namu, amma mutumin da na gani zaune a palourn namu shi ya sanya ni juyawa da sauri wanda kamun ace na ƙarisa shigewa ɗaki Mami na da fitowan ta kenan ta ganni ta qwalamun ƙira, kuma ƙiran nata ne ya tsayar da ni, ban shige ɗaki ba kuma ban juyo ba ina dai tsaye a wajan cikin taƙaici da haushin mutumin da ya zo wajan Mamina. Mami na kyakkyawa ce ta gasken-gaske, farar mace ce mai ƙaramin ruwa dan in ka ganta ba zaka ce ta haife ni ba, tana da dogon hanci da tsayin gashi wanda hakan ke sanya wasu mutanen mata kallon bafulatana, sannan tana da kyakkyawan ƙira, wanda har zuwa wannan lokacin da nima na zama budurwa amma ƙirjinta basu kwanta ba ko dan ni kaɗai ta shayar ne oho, kuma Mamina tana gyaran jikinta sosai, sannan tana da ƙugu wanda ke ɗaukan hankalin mutane dan nima a wajan ta na gado ƙugun da mazaunai, wasu in suka ganni ma har cewa suke nima na biyewa Uwata na fara bin maza dan kusan kallon da mutane ke mini kenan akan nima nasan maza na buɗe. Jin muryan Mamina ta ƙara ƙiran sunana a karo na biyu, kuma nasan palourn take so na dawo, tura baki nayi dan kuwa na tsani wannan mutumin da ke zaune a palourn namu, saboda duk cikin masu zuwa wajan ta a manyan mutane shi yake ban haushi ganin babban mutum kaman sa ga kuɗi ga kyau amma yake biyewa bin mata dan na tabbata yana da yaron da zai kusa sa'an Mami na dan daga ganinsa ya bai wa shekaru hamsin 50 baya, saboda babban mutum ne sosai kyakkyawa har da furfuransa. Wannan karon inajin muryan Mami na Juyo, cikin nistuwa nake tafiya kaman bana so, a haka na ƙariso cikin palourn fiskana a haɗe, sam-sam babu annuri ko kaɗan, kallon da Mamina ta jefo mini shi ya sanya ni tura baki ciki-ciki na ce, "Anwuni lafiya Alhaji?" Alhaji mukhtar washe baki yayi dan sosai yake ƙaunar mahaifiyata, wanda wannan soyayyan da yake mata shi ya sanya nima yake ƙaunata tamkar ƴar cikin sa, kayayyaki ne menene duk idan ya tashi zuwa sai ya kawo min, kwanaki har ya sayamun waya babba mai kuɗi, amma kuma Mamina ta maida masa ta ce ba zan riƙe waya tun yanzu ba. Amsa gaisuwan yayi yana ta saka mini albarka, amma ni fiska na ko Annuri babu balle batun amsa albarkan da yake sanya min, na tashi zan koma ciki sai ya tsayar da ni ta hanyar cewa "yarinyata Banafsha ga tsaraban ki taho ki amsa." Cikin taqaici na juyo, ji nake kaman na shaƙesa ya mutu na huta, durƙusawa nayi na miƙa hannayena bibbiyu na karɓa abinda yake miƙa mini, na ce masa, "Nagode Alhaji, Allah ya ƙara arziƙi da ɗaukaka." Yana murmushi da jin daɗin addu'a ta gare sa kullum, dan muddin zai min kyauta to ni kuma sai na suburbuɗo masa addu'a ko ban yi niya ba, cewa yayi, "Ameen ya Rabbi! yarinyar kirki Allah ya miki albarka ya albarkaci karatun ki ya baki miji na gari." Amsa wannan addu'a sai Mami na ne tayi shi cikin fara'a dan tana ƙaunar mai ƙaunar gudan jininta, yarinyar ta gudan ɗaya tal kaman stoka a cikin miya, ni kuwa tuni na jima da shigewa ɗakina inda nayi jifa da ɗan ƙaramin jakan, dan abun hannunsa ba ya burgeni. "Subhanallahi!" shi ne abinda baki na ya furta ganin wani haɗaɗɗen Qur'ani ɗan dai-dai ya faɗo ga carbin irge(counter), ga kuma sallaya ɗan ƙarami, ga kuma ruwan zam-zam duka suka faɗo daga cikin jakan. Da sauri na sunkuya ina tattara su, wanda bansan lokacin da murmushi ya kuɓuce mini ba, dan a rayuwata sosai nake ƙaunar ganin anmin kyautan Qur'ani ko sallaya, nan na dinga tsalle da murna, inata jero masa addu'an Allah ya shirya shi yasa yabar bin mata, Mamina ma Allah shiryamun ita, tuni na mance da haushinsa da nake ji, na kama murna ina jiran Allah ya kai mu gobe na nunawa Umaima. Ni da na shigo ɗaki da niyan bacci, amma ganin wannan kyauta bansan lokacin da na miƙe na ɗauro alwala na tada nafila ba, ina mai kai kuka na ga Allah na roƙawa waɗan nan bayin nasa shiriya. Ɓangaren su Mamina, ina barin palourn ta dubi Alhaji Mukhtar da murmushi ta ce, "Mun gode sosai Alhaji, Allah ya saka da alheri, ya kuma ƙara arziƙi yawa zuri'a albarka." Alhaji Mukhtar murmushi yayi ya ce, "Ameen summa ameen, Hajiya ta Amarya ta." Hararansa Mami tayi ta ce, "Za ka fara ko? To Alhaji bana son wannan magana kabar kawo mini shi." Cikin mamakin lamarin Mami ya kalleta ya c,e "Ramlatu wai me yasa kullum in nace miki ba lafiya a lamarin ki akwai wani abun sai ki musa min ki ce ba haka ba? Mutumin da yake lafiya ƙalau zai zaɓi irin rayuwar nan? In aka miki maganan aure kaman an kashe miki wani naki wai meyasa? Ramlatu ki sani ina sonki sonda ban taɓa yiwa wata ɗiya mace ba, amma dai ba komai zan barwa Allah duk wani lamari na ya iya min, ki sani kuma in anyi duniya dan Manzon Allah SAW, sai na aure ki dan na gaji da wannan rayuwa da muke yi mara fa'ida, da girmanmu da komai ga yara amma mu dinga saɓawa Allah bama tunanin abinda muke yi bashi ne, kuma za'a yi da yaranmu, wallahil Azeem Ramlatu dan ke naje Makka wannan karon dan duka addu'ata akan ki nayo sa, ina mai sa rai da fatan Allah ya amsa mini ya saita lamuranki, Insha Allahu wata shekara kema za kije dan ki ƙaro addu'an wa kanki, ni dai buri na na aureki muyi komai a inuwar sunna da lada, wannan ƙazamiyar rayuwan ta isheni." Mami da zuwa yanzu ta cika tayi fam kaman za ta fashe cikin ɗaga murya ta ce, "Alhaji Mukhtar ina ganin girmanka da darajanka, ko ba komai dan soyayyan da kake nunawa yarinyata wacce ta fi mini komai a rayuwa to shi yasa nake shiru nake cigaba da sauraranka, amma karka yarda ka fara tunanin wuce gona da iri, ko an gaya maka bansan duk abinda kake aikata min ba ne? Bansan mai kake shiryamun ba akan jama'a na? To ka riƙe girmanka, idan ba haka ba na kusa daina sauraranka, maganan aure ka aje sa a gefe, nayi aure na gama yi haka nake son rayuwata in ba za ka iya ba ka fita a rayuwata ka ƙyale ni, ai akwai mata da yawa a duniya, to kaje wani wajan ka nemi ta aure, ni ba aure ne a gabana ba." Alhaji dai kallon Mami yake kuma ba alaman ɓacin rai a fiskansa sai ma wani sihirtaccen murmushi da yake sakar mata, ga kuma fara'a wanda ako da yaushe in suka samu saɓani irin haka akan ya mata maganan aure tana bam-bami, to iya abinda yake yi kenan murmushi. Ajiyan zuciya ya sauƙe ya ce, "Allah ya huci zuciyanki Hajiyata kuma amaryata, in Allah ya so ya yarda." Cikin jin haushi Mami ta miƙe ta shige ɗakinta tare da banko ƙofa har da saka key, shi kuwa ganin haka sai yayi hamdala dan hakan yake so dama. Tashuwa yayi ya shiga ɗaya ɗakin ya wasta ruwa ya ɗauro alwala yayi nafilfilu yana mai ƙara miƙa kukansa ga Allah akan wannan baiwar Allah da yake matuƙar ƙauna, yana idar wa ya kashe wutan ɗakin ya kwanta. Washe gari da ya kama juma'a da sassafe na fito nayi shara da wanke-wanke da girki sharp-sharp, ina kammalawa na ɗiba nawa naci na koma ɗaki na shirya dan zuwa makaranta. A bakin ƙofan ɗakin Mami na tsaya ina sallama, daga ciki Mami ta amsa mun ta ce na shigo, tura ƙofan nayi na shiga, na tarar da ita zaune a bakin gadonta, Alhaji kuma yana zaune akan kujeran zaman mutum biyu dake cikin ɗakin. Durƙusawa nayi na gaishe da Alhaji, ina ƙara masa godiya sannan na gaishe da Mamina, ta amsa tana tambayan har na shirya kenan na ce mata, "Eh Mami na shirya class na 7:30 muke da." Mamina ta ce, "To Banafsha Allah ba da sa'a, a dawo lafiya, ba dai akwai kuɗin mashine a hannunki ba?" Ɗaga kai kawai nayi na juya zan fice a dakin sai naji muryan Alhaji na cewa, "Daughter tsaya na ajiye ki a makarantar ko." Kaman an bani saƙon mutuwa haka naji amma ba yanda na iya haka na fice na tsaya jiransa a qofan gidan mu. Sallama Alhaji yawa Mami akan zai tafi kuma zai fi sati bai zo ba ta kula sosai sannan baison yawan kule-kulen mutane. Kallon sa Mami tayi tana murmushi ta ce, "Alhaji kana son jan magana, kai ba mijina ba, ba komai ba kana bani doka to gaskiya sai dai kayi haƙuri dan yanda ka ganni ka biyo haka kowa ma, shiyasa na faɗa maka tun farko, ni dadiro ba shi ne abinda ya dame ni ba, kowa ya samu rabonsa yayi gaba." Alhaji kaman zai yi kuka ya ce, "Ramla kibar faɗamun irin maganan nan kin dai sani tsakanina da ke daban da tsakaninki da sauran ko? Kuma idan maganan ban aure ki kike ba mai kike ci na baka na zuba? Ai in Allah ya yarda Mukhtar sai ya mallaki Ramla ba da jimawa ba, Allah raba mu da zaman dadironcin ma." Hararansa Mami tayi ta fice a ɗakin, shima bin ta yayi dan yasan suka tsaya sai su ɓatawa Banafsha lokaci akan maganansu, har bakin motan ta raka sa ya shiga ta saka masa hulansa tana masa murmushinta mai zautar da shi ta ce, "Allah stare hanya ya kai ka lafiya, Allah karemun kai, a gaida Hajiya da yaranmu." Alhaji ji yake tamkar ya ɗauke ta yanzu ya kai ta gidan sa, a matsayin matar sa amma ba hali, murmushi kawai yayi ya ce, "Ameen Mamin yara sai kuma kin ganni." Mami ta buɗe masa madaidaicin gate namu ya fito, sanda taga shiga na da tashin motan sannan ta kulle ta koma cikin gidan. Tafiya muke sautin qira'an Alqur'ani mai girma na tashi a cikin motan, wanda da alama karatun musabaƙa ne dan daga yanayin karatun na gane. Alhaji juyowa yayi ya kalle ni ganin ina bin karatun ya ce, "Karatun ya miki daɗi kema ko daughter?" Ɗaga kai nayi kawai alaman eh dan duk da kuwa sonda yake nuna mini, da kulawa tamkar yarinyar cikin sa hakan baya hanani jin haushin sa, tunda shi ma biyewa mahaifiyata yake yi suna zubar da girmansu. Yana murmushi ya ce, "Yarinyata ce wacce ba zata wuce sa'anki ba suka yi musabaƙan, sannan ta zo ta biyu, yanzu haka tana ƙoƙarin haɗa haddan ta, sunanta Hauwa'u amma muna qiranta da Majeederh." "Allah ya ƙara basira ya albarkaci karatu" iya abinda na furta kenan dai-dai muna shiga babban gate na makarantar mu College of health Mubi, inda nake a shekara ta biyu, ina karantan CHEW, muna a semestern ƙarshe. Faɗa yamin na ƙara mai da hankali, sannan ya miƙa min kuɗi nayi na mashine amma naƙi karɓa, juyin duniya yayi da ni amma sam naƙi, ganin haka sai ya mayar da abinsa aljihu, ni kuma na sauƙa tare da masa addu'an a isa lafiya, shi kuma yaja motansa ya tafi. Ajinmu na ƙarisa inda na tarar har malami ya shiga wanda ke ɗaukan mu environmental care, nan na samu waje na zauna ina sauraran karatu, sai da muka share hour guda har da ɗori kamun malamin ya juya ya fice, ina ƙoƙarin miƙewa naji mutum ya zauna gefe na, juyawa nayi ganin Umaima ce sai na haɗa fiska na wuce na fice a ajin, ina tafiya ta sha gabana ta kama kunne tana cewa, "Haba masoyiya ta Banafshaty, kiyi haƙuri mana." Ko kallon ta naƙi yi, na juya zan ci gaba da tafiya kawai sai ta rungume ni ta ce, "Wallahi masoyiya ba laifi na bane, Ya DANISH ne ya hanani zuwa gidanku ya ce shi zai kai ni makaranta, kuma kema kinsan halinsa in naƙi zai bulale ni ne, ni bansan jaraban da ya saka shi dawowa jiya Alhamis dare-dare ba, mutumin da juma'a ma sai yamma yake dawowa." Cikin gamsuwa da magananta na ce, "Shikkenan Umaima ya wuce, shi kuma mai niyan raba mutunci da soyayya Allah ya shirya sa, nima yau Alhajin da nake gaya miki inajin haushinsa sosai shi ya kawo ni." Nan muka wuce ƙasan wani bishiya muka zauna, har na bata labarin kyautan da ya kawo mini da kuma labarin yarinyar sa da ya bani. Murmushi Umaima tayi ta ce, "Allah kuwa Banafsha wannan bawan Allahn kaman dan Allah yake son Mami." "Hmmn! Umaima kenan, in da gaske yake sonta ai sai ya aure ta, amma yake biyo ta har ya dinga kwana a gidanmu, na faɗa miki duk cikin masu zuwa wajanta shi kawai ke yin kwana har fin 1 wataran fa sai ya kai kwana huɗu har da ɗaki ɗayan can nasa ne, ni ban ma san shi kuma me yake cewa matan sa ba da har yake kwanaki a gidanmu, Allah na tsani mutumin sosai." Ganin raina na ƙoƙarin ɓaci sai Umaima ta kawar da maganan muka kama wani, har muka koma class aka ci-gaba da lecture, mu ne bamu tashi ba sai ƙarfe ɗaya ciff na rana, inda ana tashi ni da Umaima muka fito muka nemi mashine muka yi gida ba ɓata lokaci. *** INA KUKE MASU SANA'A, SANA'A MAGANIN TAQAICIN RAYUWA. SAUQI YAZO MUKU HAR INDA KUKE DOMIN WANNAN BA IRIN NA SAURAN BANE Ga mai buqata a tallata masa hajar sa ko kuwa dai sana'ar sa to yai maza ya garzayo ga uwar batoorl mai tallata haja , a rahusa mai sauqi domin kuwa har da alakoro ina yi. KU TUNTUƁE NI A WANNAN LAYIN NAWA 09161720046 WHATSAPP TELEGRAM 07015870735 WhatsApp ko call Ko Gmail nawa yarmalam96@gmail.com Akan rahusa mai sauqin gaske, sai kunzooooooo🤝 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE My Queen (Aunty Mairo tawa) My Dearest (real mum batoorl) Hafsat Umar Surryh baby اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 11 _ 15 Sanin halin ƴan anguwanmu iyayen sa ido sai muka roƙi mai nafen ya kai mu har ƙofan gida, hakan kuwa aka yi kaman yanda muka buƙata, muna sauƙa muka yi sallama, Umaima ta juya ta nufi gidansu, ni kuma na shige gidanmu. Ashe mu bamu san tun sauƙanmu a mashine ya Danish dake staye a ƙofan gidansu yana kallon mu ba, Umaima ta zo shigewa gida kenan, kaman daga sama cikin stawa aka ce mata, "Keeee! me ya haɗa hanyar ki da na yarinya mara tarbiyan can?" A razane ta juyo jin muryan ya Danish, ita duk stammaninta ya koma Camaroon ɗazu, ashe yana gida, tuni hanjayen cikin Umaima suka ɗuri ruwa ganin irin kallon da yake jifanta da shi. Ya Danish kenan, saurayi chocolate color kyakkyawan gaske, wanda kana ganinsa kaga Fulanin Camaroon dan hatta dogon gashin su shi ma ya bari, idan kaga kansa sai ka ce na wata mace mai tsayin gashi ce, mutum ne mai zafin hali ga kuma ji da kai baya son reni ko kaɗan, ba shi ne babba a gidan ba amma za ka ranste shi ne babban su saboda halinsa. Umaima kaman za tayi kuka ta ƙaraso gabansa ta stugunna tana cewa, "Kayi haƙuri yaya ba zan ƙara ba." Wani mugun kallo ya aika mata kaman zai kifa mata mari, cikin ɗaga murya ya ce , "Idiotttt! ɓace mun a gani kamun na ɓalla ki, kina haɗa hanya da ita salon ace kema ba ki da tarbiya ko? kina son ki ɓata mana sunan gida." Miƙewa Umaima tayi da mugun gudu, bata jira ya gama faɗan abinda zai faɗa ba ta shige gidannasu tana haki. UMMU-KHULTUM ALIYU MUHAMMAD YAWONDE! Shi ne asalin sunan ƙawata Umaima wacce ta kasance ƴar Auta a ɗakin Umma Sabeera. Matan Abbansu Umaima, Alhaji Aliyu Muhammad yawonde biyu ne, Umma Sabeera da Ummu-khultum wacce ƙawata Umaima take takwararta, Ummu ta kasance mace mai fara'a da sanyin hali, ga sanin ya kamata ga kuma haƙuri ba ruwanta haka yaranta ma ba ruwan su, saɓanin Umma Sabeera da take masifaffiya ba haƙuri kuma bata ƙaunar kowa sai nata bata son reni amma yaranta basu iyo halinta ba. Umma Sabeera ita ce Uwar gida, yaran ta huɗu, Yaya kabeer wanda muke qira da Yaya babba, sai ya Danish, sai Ya mus'ab sai Autar su ƙawata Umaima, duka yaran Umma Sabeera sanyin hali ne gare su tamkar Ummu ce mahaifiyar su ba Umma ba, musamman dai Umaima takwara ga Ummu wacce kamun awa Ummu takwarar ma sai da aka sha daru da Umma Sabeera akan ta ya za'a sanya wa yarinyarta sunan kishiyar ta. Ya Danish shi ne kusan ya ɗauko rabin halin Umma Sabeera amma dai ba duka halin nata ya ɗauko ba, dan shi yana da haƙuri kawai ya cika faɗa ne da kuma rashin son reni. Ummu kuma yaranta uku 3 ne, Yaya Farooq wanda yake babban yaronta sai kuma Yaya sadeeq sai kuma ƴar Autar ta Balkisu wacce ake qira da NANA Yaran Ummu ba ruwan su kaman Ummu haka suma suke da sanyin hali, idan ka shigo gidan za ka ɗauka duka yaran gidan yaranta ne, dan ba ruwan Ummu da banbanci ko wani abun, duk da Umaima ta girmi Nana, amma duk abinda za ta yiwa Nana sai ta yiwa ƙawata Umaima, wani lokacin ma sai ta saya ma Umaima abu ba tare da ta saya wa yarinyar ta ba. Tun da na taso a anguwan nan na ganmu kuma naga Ummu kan shigo gidanmu lokaci zuwa lokaci inda har ƙawance ya shiga tsakanina da Umaima tun muna yara har Allah yasa muka girma, amma Umma Sabeera da ya Danish kwata-kwata basu son ganin Umaima tare da ni, ita kuma Umaima ƙaunata take dan Allah soyayya ce da aminta stakaninmu ba kaɗan ba, tun daga primary school har secondary har zuwa yanzu da muke matakin gaba da secondary duka makaranta ɗaya muke yi kuma aji guda, haka a ɓangaren Arabic ma makaranta guda muke, ƙawata Umaima na da ƙwaƙwalwa nima hakan shiyasa ko a makaranta kullum mune a gaba. Duk gidan nasu kyawawa ne dan Abba suka ɗauko amma kyawun ya Danish ya fita daban dan shi kaman ya haɗa dangi da baƙaƙen larabawa amma bafulatanin Camaroon ne su gaba da baya, Abba da Umma Sabeera ƴan camaroon ne Ummu ce kawai ƴar Nigeria anan cikin Mubi amma ita ma bafulatana ce. Kowa na sona a gidan su ƙawata Umaima, banda Umma Sabeera da kuma ya Danish wanda su biyun nan har ƙirana da sunan da nafi stana a rayuwata suke yi, wato ƴar karuwa. Ya DANISH ko kallo na yayi sai ya harare ni ko kaɗan baya ko son ganin ina shiga gidansu, shiyasa wani lokacin Mamina ke hanani amma Abbansu yakan stawatar masa shi da Ummansa akan su daina tsangwamata, amma Umma Sabeera in ta tashi sai ta kaada baki ta ce ai Abba so yake shima yabi karuwar Uwata, shiyasa yake haɗani da yarinyanta dan haka ba da ita ba sai tasa Ya Danish ya dinga dukan Umaima akan ta daina kula ni, amma Umaima ko me zai mata sai ta shigo gidanmu kuma sai dai in bata ganni ba sai ta mini magana, ran da aka ci sa'a Ummu na gida to ko me Umma Sabeera za ta ce bata bari ya Danish ya taɓa Umaima, dan tana sonta sosai wanda Umma Sabeera ke faɗin, wai soyayyan na munafurci ne. Ya Danish mutum ne da bai damu da yawan magana ba, kawai dai in har ya ƙi abu to ya ƙi sa ne ko hanya baya son haɗawa da shi, wanda kuma abinda bai sani ba shine nikam ba iya shi na tsana ba gaba-ɗaya maza na tsane su a rayuwata, da ya kwantar da hankalinsa da stangwamata da yafi masa dan nima na stane shi fiye da tunanin mai tunani tun ranar da ya fara cemun ƴar karuwa, tun ranan ya fice mini a rai. Ummu ganin Umaima ta shigo gida da ghdu kaman an biyo ta, sai leƙa bayan Umaima take yi dan taga wa ya biyo ta amma bata ga kowa ba, kallonta tayi ta ce, "Umaima lafiyanki kuwa? Ke da wa da gudu haka?" Umaima na haki ta ce, "Ummu wallahi ya Danish ne ya biyo ni." Kaɗa kai kawai Ummu tayi ta ce, "Nasan za'a rina, wai an saci zanin mahaukaciya, to Allah ya kyauta kawai, Danish ko kaɗan baya ji bansan me Banafsha ta ci masa ba, dan nasan ba zai wuce dan ita ya biyo ki ba, wuce kije ki huta ki ɗiba abinci a kitchen ki ci, shi kuma zai shigo ya same ni." Amsawa Umaima tayi ta wuce cikin ɗakinsu ta sauya kaya ta watsa ruwa tayi sallah sannan ta ɗibo abinci ta dawo palourn tana ci tana kallo sai ga Nana ta shigo, kallonta tayi ta ce, "Ke kuma daga ina?" "Tayani tambayan ta dai", faɗin Ummu da ke zaune ita ma tana kallon. Nana tura baki tayi ta ce, "Daga gidan babban yaya nake", tana faɗa ta wuce ɗakin su. Ni kuwa ina shiga gidamu na tarar Mamina tana shanya kaya na da ta gama wanke wa, rungumeta nayi na ce, "Sannu da aiki Mamina, maimakon ki bari idan na dawo nayi ko da gobe ne tunda bamu da class." "Parrot daga dawowa sai surutu wuce ciki ai na gama wankin" faɗin Mamina tana min murmushinta mai stada. Nima murmushin nayi na shige ciki ina jin farin ciki haka kawai bansan dalili ba, Uniform nawa na cire sannan na fito palourn namu na tarar komai a gyare staff ko ina sai tashin ƙamshi yake kawai, "Uhmn! Mamina kenan ga tsafta ga son ƙamshi, ga kuma kyau Allah barmun ke Uwata ya kuma dai-daita rayuwarmu", abinda na faɗa kenan na wuce kitchen namu, abinci na ɗibo shinkafa da miya da ya ji ice-fish ga coslow a gefe, ɗan kaɗan na ɗibo kaman an roƙo, wanda ko yaro aka bawa zai cinye tass bai ƙoshi ba, na dawo palour na zauna ina addu'an kar Mamina ta shigo ban fara ci ba ta gane ban ɗibo da yawa ba. Nasa cokali zan fara ci sai kawai Mami ta shigo, rau-rau nayi da idanuwa na kana gani kaga na mara gaskiya, kallo ɗaya Mami tamini da ni da plate ɗin dake gabana ta girgiza kai ta wuce ɗakin ta bata ce komai ba, ganin ta shiga ɗaki da mugun sauri nima nayi nawa dakin, naci abincin na sha ruwa sannan na tashi na ɗauro alwala nayi sallahn azahar. Kyautan da Alhaji ya kawo min na jida na kai wa Mamina, nan ta dinga jin daɗi tana masa addu'a, sai ta ce, "Yauwa BANAFSHA kinga ma kin tuno min, dama ya ce na tambaya makarantar ku ana musabaƙa ne ko kuwa ba kwa yi, in bakwa yi sai a sanja miki wai dan musabaƙa na ƙara sa yaro zama mai hazaƙa da ƙoƙari." "Uhmn! Mami nifa ban cika son musabaƙan nan bane, dan ana ce masa wai karatun riya ko kuma gasar karatu wanda aka maida shi tamkar abin jan fitina, a makarantar mu ana yi nice kawai bana so dan kwanaki ma Umaima ta ce mu yi naƙi, duk da kuwa malaman na zaɓan mu, amma sai mu bada uzuri." Murmushi Mami tayi ta ce, "Eh tom kinga dai cewa kika yi wasu ne suke faɗin hakan, ba wai duka mutanen duniya ke faɗa ba, amma yanzu ke a me kika ɗauki musabaƙa akan ra'ayinki?" "Ni Mami na ɗauke sa tamkar dai wata hanya da dama da ake bawa ɗalibi dan ganin yan inganta karatunsa, a zahiri za kayi karatu ne dan kar ka faɗi amma a ainafin niyar abun an saka shi ne dan ka ƙara mai da hankali akan karatu." "Yauwa yarinyar kirki Nana Faɗima batoorler, kin fahimta da kyau haka nake so dama ako da yaushe tunanin ki yasha ban-ban da na sauran mutane, ta ko wacce siga ki kasance kin ɗauko halayyan mai sunanki, abinda nake so ki ƙara akan wannan tunanin naki shi ne ki ɗauko hadisi na farko a cikin arba'una Hadith ki ƙara a kai." Kallon Mamina nayi na ce, "Mami hadisin na nufin dai komai ana yin sa ne da niya kuma komai kayi yana tafiya ne da niyan ka." "Good girl! Kinga kuwa ashe in kika ƙuduri naki niyan daban ba dan riya ba ko gasa kinga ke daban saura daban, Allah subhanahu wata'ala yace "muna duba ne zuwa ga zuqatan ku ba jikkunanku ba" kinga kuwa abinda ka ƙudurta a zuciyanka shi ne abu na musamman da Allah zai tuhume ka akai." Murmushi nayi cikin gamsuwa da zancen Mami na na ce, "Shikkenan Mami, na fahimta in Allah ya yarda zan gyara niya na." "Yauwa ina so wani musabaƙan ya zama da ke aciki, sannan ki dage ta yanda al'umman Annabi SAW za suyi alfahari da haihuwanki, ki kulle idonki ki toshe kunnenki kawai ki fuskanci abinda kika sa a gaba inhar dai bai saɓawa mahaliccin ki ba, ki kula sosai a ko ina ki riƙe mutuncin kanki dan shi ne ƙimarki da darajarki a gidan mijinki, Allah ya miki albarka ya albarkaci dukkan rayuwanki FAƊIMAH." Duk maganan da Mamina ke yi idanuwa na kan ta ina kallon ta ina mamaki a zuciyata da lamarin Mamina, anya lafiya? Mamina tana da ilimin boko da Arabic fiye da tunani na, Mami tasan hukuncin ko wanni laifi da ayar da aka sauƙe hukuncin barin ma dai Zina, amma me yasa Mami na ta zaɓi rayuwar karuwanci? Me yasa ta zaɓi take sanin ta? Me yasa ta kauda kai akan ayar Allah? Ta zaɓi zubar mana da mutunci akan adana mana shi, sannan sai tace na riqe mutunci na, koma dai menene addu'a ita ce maganin ko wacce iriyar cuta da musiban rayuwa, in Allah ya yarda ni kuma zan dage da kai kukana ga Allah na dage da addu'a... Maganan da Mamina ke yi shi ya dawar da ni daga duniyan zancen-zuci zuci da na faɗa, "Banafsha me kike tunani haka? Cewar Mamina idanuwanta a kai na. Buɗe baki na yi da niyan faɗa mata amma sai na kasa kawai na ce, "Mami ina tunanin assignment da aka bamu ne gashi hangout na yana wajan Umaima." "To maza tashi kije ki karɓo daga nan ki gaida min Ummun ku." Miƙewa nayi na tafi ɗakina dan saka hijab amma ina shiga ganin mayafin dogon rigan material dake jikina sai na fasa ɗaukan hijab, na ɗau mayafin tunda dai gidan su Umaima kawai zan je. Ina fitowa Mami ta kalle ni ganin mayafi na saka ba hijab ba sai tace "Banafsha ke kuma ina za ki da mayafi ba hijabi?" "Mami Allah ba inda zan je, iyakaci na gidan su Umaima kuma ina karɓa zan dawo." Mamina ta ce, "Amma dai kinsan gidan su Umaima ba su kaɗai bane ko, kinsan akwai maza ba iya mata ba ne, kuma ba muharramanki ba, yanzu ko muharraminka ma ba ko wani irin shiga ake so ka yi ya gani ba balle wanda ba muharraminka ba, maza koma ki sako hijabinki bana son shirme, yarinya ta girma bata san ya girma ba." Marairaicewa nayi na ce, "Allah yanzun nan zan dawo Mamina." "Tom maza kiyi sauri ki dawo, kinsan ba son fitanki da mayafi nake ba tunda kema kinsan ƙirar da Allah ya miki yarinyar fuk-fuk kaman kazar gona." Murmushi nayi kawai na fice tun da dai ta barni na tafi hakan, amma inajin kunya dan nasan nufin Mami, Allah ya wadata ni da arziqin mazaunai wanda kaga ƙuguna ka ranste nasan maza, ƙirji na kuwa Masha Allah dan suma Allah ya azurta ni da su, shiyasa Mamina idan ta tashi take cemun kazar gona (brolas) fuk-fuk, ga shi idan ina tafiya komai na jikina mostawa yake, kuma dai ba rigima nake ba haka Allah yayo ni. Da sallama na tura ƙofan gidan na shiga, kaina a qasa na tunkari hanyan shiga babban palourn gidan, ban ankare ba kawai na ji ni nayi karo da mutum, nayi baya zan faɗi haka wanda muka yi karon nan ko ya hanani faɗuwan ta hanyan tare ni, sai da na zauna da ɗuwawuna daɓass a ƙasa. Ƴar ƙaramar ƙara na saki na ce, "Washh! Wayyo Allah!! Mamina mazaunaina sun yi targaɗe." Stakin da aka ja shi ya sanya ni dawowa hayyacina, na ɗago fiska a hasale cikin tarin taƙaici da masifa, duk da ganin wanda muka yi karo da shi ɗin amma hakan bai sanya ni shanye haushin tsakin da yamun ba, da ƙyar na miƙe ina riƙe ƙugu na ce, "Mstww!! Mutun ba abinda ya iya sai son taɓawa mutane jiki wai ahakan shi kamemme ne kuma nagari, to kai ɗin ma dai ba wani na kirki ba ne", ina gama faɗa na yayiɓo mayafina da yayi gefe na miƙe zan wuce amma sai ya yi saurin shan gaba na yana ƙaremun kallo sama da ƙasa. Tufar da yawu yayi sannan ya ce, "ƙaramar ƴar iska ba ki da abinda zan kalla ma balle na taɓa." Hararansa nayi cikin ɓacin ran abinda ya mini, nima na tufar da yawu kaman yanda ya yi, amma yawuna direct sai akan takalmin sa, na murguɗa masa baki tare da harara na ce, "Alhamdulillahi tunda ni ƙaramar ƴar iska ce, kai kuma sannu babban ɗan iska mai digiri mai son taɓa mata to wallahi dan kaji Banafsha ƙwalelen ka ce, dan ni ba irin su bane nafi ƙarfinka, sai gani sai hange daga nesa, ƙwalelen biri da hantar kura." A zuciye Ya Danish ya ɗaga hannu da niyan sauƙe mini mari, har na runste ido ina jiran sauƙan mari sai muryan Ummu ne ya sauƙa a kunnenmu, wanda yayi nasaran tsayar da shi Allah ya taimake ni, cikin ɓacin rai ya juya yabar wajan yana min kallon da nasan fassaransa bai wuce karki sake mu haɗu ba ne. Ummu ƙarasowa tayi ta ce, "Banafsha mai Danish ya miki? Naji ihunki." Tura baki nayi na faɗawa Ummu yanda aka yi, nan ta ƙara bani haƙuri ta ja hannuna muka shige cikin gidan ina ji a raina kaman na koma na ƙarisa gaya masa maganan dake rai na tunda shi ya ce babban ɗan iska ne shi, ni ba ruwana ka gayamun A na ƙarisa maka har Z, bancika magana ba amma aka taɓoni antaɓo stuliyan dodo, ba wani kirki bane da ni, na iya tijara sosai. Umaima da ta shigo palourn hannun ta riƙe da wayar Ummu da ake ƙira, miƙa mata tayi Ummu ta amsa tayi ɗakinta ita kuma ta zauna gefe na tana cewa, "Masoyiya me ya faru?" Hararanta nayi na ce wannan mugun yayan naku mana shi yasa nayi targaɗe a mazaunaina, yanzu har ji nake sunamun ciwo, kuma Allah sai na rama." Umaima da ta fahimci wanda nake nufi sai tayi murmushi ta ce, "ya Danish ba shi da kirki ko kaɗan nima ɗazu saura kaɗan ya sanya ni na rasa haƙora na wai akan ya ganmu tare, bansan me kika tsare masa ba wallahi ya cika takura." Taɓe baki nayi nace "oho masa kuma haka zai ganni ya barni dan ni muruccin kam duste ne atou, kuma in bai da kirki ne nima ban da shi, ni ko mutunci ma ban da shi, idanuna ba ruwa sai na masa stirara tsaff idan yayi wasa, dan ba kunyan ganinsa ba wando zan yi ba, ai shi ya nema, wa ya ce ya ƙirani yar iska,ya ce ƴar karuwa hakan bai ishesa ba sai ya ƙara da ƴar iska, to wataƙila dai da shi na taɓa iskancin." Umaima tana dariyan maganana ta ce, "Masoyiya ko dan ya ganki ba hijabi ne ya rikice har ya sanya kika targaɗa mazaunanki? Ya ga kaya" ta ƙarishe maganan tana wani dariyan. *** INA KUKE MASU SANA'A, SANA'A MAGANIN TAQAICIN RAYUWA. SAUQI YAZO MUKU HAR INDA KUKE DOMIN WANNAN BA IRIN NA SAURAN BANE Ga mai buqata a tallata masa hajar sa ko kuwa dai sana'ar sa to yai maza ya garzayo ga uwar batoorl mai tallata haja, a rahusa mai sauqi domin kuwa har da alakoro ina yi. KU TUNTUƁE NI A WANNAN LAYIN NAWA 09161720046 WHATSAPP TELEGRAM 07015870735 WhatsApp ko call Ko Gmail nawa yarmalam96@gmail.com Akan rahusa mai sauqin gaske, sai kunzooooooo🤝 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Mrs Isham Maman Abdallah(mutan Nijar) Autar Marubuta Ɓingel kabi اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 16 _ 20 Hararanta nayi na ce "Munafuka mai ƙarawa wuta fetur, to ni me ma ya fito a jikina da za'a gani? Uhmñ! Inma dai hakan ne to ya sani ƙwalelensa ya gani, wannan jikin yafi ƙarfin wanda bai iya sarrafa kalaman bakinsa ba, banda lokacin maza balle irinsa mata-maza, mstwwww! Za ki sa ma raina ya ɓaci wallahi" na faɗa ina kai mata bugun wasa a cinya. Umaima na dariya ta ce, "Auchh! mai targaɗe a mazaunai nima targaɗa mini cinya za kiyi ne, ki cuci mijina da yarana? Ayi haquri a mana afuwa ni da yayana kar ran masoyiya ya ɓaci, yanzu dai ya Maminmu take?" "Mami na can gidanta, ita ma kinsanta da zuciya yanzuma sai da nace assignment aka bamu, hangout nawa na hannunki kamun ta barni na shigo, kuma kaman tasan mugun nan yana gari, fa shi na mata ƙarya kuma Allah ya kama ni, Allah na tuba. Umaima ta murmusa ta ce, "Ya Danish ai sai shiriyan Allah, yanzu dai tashi muje na gaisar da Mami kamun sai mu wuce wajan gadan kwaccam yin aikan Ummu, dan tsakanin yau da dare ko gobe da safe Umma da Abba za su dawo kuma kinsan da safe muna zuwa Tahfiz." Taɓe baki nayi ban ce komai ba na miƙe ina faɗin "mu tafi to." Umaima ɗauko mayafi tayi ta yafa ta nufi hanyan fita tana cewa, "Masoyiya mu tafi kuma kin staya?. Konawa nayi na zauna ban ce komai ba, sai Umaima ta ce, "Banafshaty zaman me kuma? Ko dai har yanzu mazaunan ne?" Hararanta nayi na ce, "Yanzu ke dai kinsan ba da mayafi za mu fita ba to me na saka mayafi? Ki koma ki sako hijabi nima muna zuwa gidan Mami zan sanja dan tun daga gida ya Danish yamin rashin mutunci, idan na fita kam nasan sai an kusa jefeni a tsaye." Umaima babu musu ta juya ta koma ta sako hijabi har ƙasa kamun nan na miƙe muka fice a palourn, duk sauri-sauri muke dan kar ya Danish ya ganmu domin staff zai hana mu fita tare, Allah ya taimake mu har muka fice a gidan bamu gansa ba, daa sallama muka shiga gidan Mami amma ba kowa a palourn dan haka ɗakin Mami muka nufa, kamun mu ƙarisa ɗakin sai Mami ta fito tana murmushi ganinmu tare. "Yar Mami an sakoki gaba sai kinyi rakiya ko?" Mami ta faɗa tana kallon Umaima. Murmushi Umaima tayi ta ce, "A'a Mami nice na ce zan zo gaishe da Maminmu." Mami ta ce, "To Allah ya miki albarka ƴar Mami." Tura baki nayi na ce, "Mami albarkan ita kaɗai banda ni?" Umaima dariya ta sanya tana kallona ta ce, "Masoyiya ashe mun koma kishiyoyi?" Hararan ta nayi na marairaice ina kallon Mami, amma Mami ko kallona bata yi ba ta ƙaraso palourn, nan muka zauna Mami na ƙara tambayan mu game da karatu. Can ganin lokaci na tafiya sai na dubi Umaima na mata magana aikanmu da Ummu ta yi. Mami kallon ikon Allah take ta ce, "Yaran nan dama Ummun ku ta aike ku kuka tsaya aikin surutu baku tafi ba? To Allah yasa ta zane ku maza-maza ku tashi kuje kar Magrib ya same ku a waje." Miƙewa muka yi na ɗauko hijabi na muka fice a gidan muka nufi shagunan kan gadan kwaccam, muna tafiya muna hira, ina murmushi na ce, "Umaima, Mami dai ta ce musabaƙan wannan shekara ayi da mu." Duk da akan hanya muke amma farin cikin Umaima bai ɓoye ba kaman ta ɗaga ni sama haka ta dinga murmushi, har da ɗan tsallenta ta ce, "Kai amma Allah dai ya bar mana Maminmu, Alhamdulillahi tayi convincing naki yanzu kam kin cire wannan banzan ra'ayin naki, in Allah ya yarda kuwa bana da mu za'a je Makka dan sai mun lashe." Hararanta nayi na ce "Yanzu kin ga irinta ko, ba zaki ce bana sai mun haɗa ba wai da mu za'a je Makka, yanzu damuwanki kyautan da zaki samu ba karatun ki ba ko?" Umaima ta ce, "Uhmn! Masoyiya ba zaki gane ba, tabbas inaso karatu na ya kammalu zuwa yanzu ya kamata ace mun haɗa, amma ina buƙatar zuwa Makka sosai dan akwai kukokin da nake so na kai wa Ubangiji na a ƙasa mai starki duk da anan ɗin ma ina yi kuma bana cire ran yana amsuwa amma can ɗin daban ne, sannan na kai ziyara ga ma'aiki SAW a madinatu.' Idanuwa nane suka kawo ƙwalla jin abinda Umaima ta faɗa, domin kuwa ni ce na fi kowa buƙatan zuwa ƙasa mai tsarki, ni ce nake da kukokin da zan kai, share hawayen da ya zubo min nayi dai-dai mun iso shagon. Umaima ce ta miƙa kuɗi aka bamu abinda muka zo saya muka juya cikin nistuwa muke tafiyanmu, muna tafiya dai-dai majalisan ƴan sa idon anguwanmu sai wani matashi ya taso ya tare mu yana kallona yana magana, ya ce, "Yarinya mai kyau da ƙira, gàskiya ni kin mini kuma ba ruwa na da mahaifiyarki karuwa ce ko me ni inasonki a haka." Wani gululun baƙin ciki ne da kuma taƙaici suka taru a zuciyata suka min yawa wanda cikin ƙunan zuciya na nuna shi da yasta amma kamun nayi magana Umaima ta riga ni, ta ce, "Kai wani irin ɗan akuya ne? Ko shaye-shaye kake yi da har ka samu confidence na tsayuwa a gabanmu kana gaya mana baƙin magana kai waye?" Cikin ɓacin rai ya juya kan Umaima ya ɗaga hannu da niyan zai mare ta yana cewa "Ke ubanwa ya kasa da ke? Ki bari wacce na yi da ita ta bani amsa." Hannun nasa da ya ɗaga zai mare ta na buge nayi jifa da shi cikin tsananin fushi na nuna sa da yasta na ce, "Ubanka halliru mai bin gidan matan mutane kwartanci ne ya kasa da ita, kai akwai cikakken karuwa ma irin ubanka? Bai bar yara ba haka manya sannan matan aure, ɗan akuya ƙaramin mara mutunci baƙon bariki, waye aka gaya maka baisan ubanka na kwartanci ba kuma kuɗin da yake da shi kuka gagara ci kuna fatan mutuwansa waye baisan kuɗin tsafi bane? Ko an gaya maka ba'a san an kamasa da stohuwar da tayi jika da shi bane? Ka kama kanka ni ba sa'an yinka bane nafi ƙarfin ubanka balle kai, ka ƙara furta kalmar banza akan mahaifiya ta wallahil Azeem za kasha mamiki, tunda kai baka san darajan iyayenka ba to na fi ka rashin mutunci, jahili mara tarbiya, msttwwww!" Kama hannun Umaima nayi muka yi gaba yana tsaye cikin tulin kunya da ɓacin rai, ganin har mun kusa ɓacewa ganinsa cike da isgili ya ɗaga murya ya ce "ƳAR KARUWA ki sani ko kin ƙi ko kin so sai na je garin daɗinki dan ki sani asirinki zan rufa miki tunda ba wanda baisan cikin shege aka yi aka haife ki ba, kuma kema ƙafan uwar taki kika bi na karuwanci." Maganansa ba ƙaramin sosamun zuciya yayi ba, musamman da ya sheganta ni, ai babu shiri a fusace na juyo da niyan komawa na ƙwada masa mari ina hawaye amma sai Umaima ta riƙe ni, ta ƙi barina na koma, ina ja tana jaa na, cikin taƙaici kawai na fashe da kuka na ƙwace hannuna nayi hanyan gidanmu ina kuka mai cin zuciya, saboda mahaifiyata ita ce lago na, ina da saurin kuka musamman akan irin waɗannan maganan, amma idan ba haka ba nima dai-dai nake da kowa ka mini na maka. Umaima fasa kai aikan tayi ta biyo bayana tana ƙiran sunana, tana ban haƙuri tunda tasan shiga da kukan ba maganin komai zai mini ba, sai dai ma ya ƙara min wani damuwan tunda yau ba'a ji ni da Mamina ba, amma naƙi sauraran Umaima balle na tsaya. Ina saka ƙafana a cikin palourn mu na kuma yin karo da mummunan abinda ya fi mini maganan da aka gayamun ciwo, Mamina tare da wani ƙaramin yaro suna shafa juna, cikin hanzari na juya ina ƙara sautin kukana wanda kana ji kasan abu ne mai ciwo ke cin zuciya na. Umaima za ta shiga amma sai na riqo ta dan banson ta ga abinda na gani, ita kuma ganina sai bata damu da ta shiga cikin ba, ta biyoni kawai muka yi gidan su ina kan kuka na mai stuma zuciya. Wannan matashin juyawa yayi majalisar su yana ta kan kumfan baki, sauran da basu san abinda babansa ya aikata ba sai da nayi magana, cewa suke "Garba wai dama abinda stoho yake yi kenan?" Cikin ɓacin rai ya miƙe yabar majalisar ba tare da ya tanka musu ba, amma ya ƙuduri aniyan sai ya ƙuntatawa ƴar karuwa tunda ta ci mutuncin ubansa ta tona masa asiri, su kuma ganin haka suka ta dariya suna cewa, "A lallai dole mu hankalta tunda Halliru na danne mata da yaran mutane" in suka faɗa sai su kwashe da dariya. inda sauransu kuma ke ta kan maganana wasu su ce sunji daɗin abinda Garba ya mini wasu kuma su ce basu ji daɗi ba. Daman ita duniya haka take, wannan na sonka babu dalili, wannan na ƙin ka babu dalili. Da kuka na shiga gidan su Umaima inda kai tsaye na wuce ɗakin su, Ummu tun shigowanmu ta kalleni kawai ta girgiza kai dan in ta ce bata tausayin Banafsha to tabbas tayi ƙarya, yarinya ƙarama baƙin ciki na neman kasheta kullum abu ɗaya kuka-kuka. Umaima tana ajiye wa Ummu aiken ta juya za ta tafi ɗakinsu wajen Banafsha, sai Ummu ta tsayar da ita tana tambayanta me ya faru? Umaima kaman za ta yi kuka ta buɗe baki ta bawa Ummu Labarin duk abinda ya faru ta ɗaura da cewa, "amma Ummu bansan me Banafsha ta gani ta fasa shiga gidan Mami ba." Ummu jinjina kai kawai tayi cike da ɗimbin tausayin Banafsha ta dubi Umaima ta ce, "Je ki rarrashe ta ina zuwa ko." Umaima shigowa ɗakin da nake ciki tayi ta zauna gefena tana bubbuga bayana cikin sigan rarràshi tana faɗin, "Banafshaty dan Allah kiyi haƙuri hakanan ki daina kukan nan, kanki zai yi ciwo fa." Cikin kuka wanda har ya dishar min da murya na ce, "Haba Umaima! Haba Umaima! Yanzu ke hakan ya miki? Kullum haƙuri kawai kullum abu ɗaya haƙuri kawai? Ba za ki ce mini wani abun ba?" Umaima ta ce, "Banafshaty bayan haƙuri me kike so? Ko akwai kalman da kike buƙata na faɗa miki wacce ta fi haƙuri ne a halin da muke ciki yanzu?" Stayar da kukan nayi ina kallon idon Umaima na ce, "Dan Allah ko sau ɗaya ku ce mini na shiga duniya, ko kuma na kashe kai na, dan Allah Umaima ki ce na kashe kai na zan huta" na faɗa ina haɗa hannayena tare da sakin kuka mai matuƙar cin zuciyan duk mai saurarona, dan ni kaɗai nasan zafin da nake ji a zuciyata, duniyan gaba-ɗaya bata mini daɗi, ji nake kaman na hau kwalta mota ya take ni ko zan huta, ana storon mutuwa amma ni a halin da nake ciki nafi ƙaunar mutuwa fiye da rayuwata, abin ya koma har ƴar shege ana ƙira na, tuna abinda Garba ya faɗa mini da abinda na yi tozali da shi a gidan Mamina sai na kuma fashewa da kuka mai tsanani, tun kamun Umaima ta yi magana na tari numfashinta na kuma cewa, "Dan Allah ke ma kiyi haƙuri, kar ki ce mun a'a kinji Umaima, Please ki ce na kashe kai na dan Allah." Umaima kallona tayi cikin karaya da matuƙar tausayina ta ce, "Banafshaty naji roƙon ki, amma kamun nan dan Allah ki saurareni." Zuba mata idanuwana da suka jiƙe da hawaye nayi, wanda kana ganinsu kaga tsantsar damuwa da raɗaɗin da nake ciki ko ban faɗa maka ba, ka kalli idona kasan ina fatan mutuwa wa kaina akan wannan rayuwa. Numfasawa Umaima tayi, idanuwanta sun cicciko da ƙwalla ta ce, "A cikin shika-shikan Musulunci guda biyar 5, na huɗunsu shi ne Zakka, nasan kinsan da wannan Banafshaty, Zakka ba yana nufin iya na dukiya ko dabbobi ne Zakka ba, ki sani a cikin halayyanmu akwai Zakkan da za mu dinga fitarwa wanda yake a matsayin haƙuri, haƙuri kuma halin Manzon Allah SAW ne,halin da Allah da Manzon sa suka fi so, to tabbas har abada in baka mutu ba sai andinga binka da kalman haquri dan tunatar da kai ɗaya daga cikin shika-shikan Musulunci kuma guda daga halayen fiyayyen halitta Rasulullahi SAW, a cikin ƙur'ani mai girma, Allah ya ambaci haƙuri ba adadi, ga Annabi SAW, da kuma mu al'umman Annabi SAW, akwai inda Allah ya ke faɗa wa Rasulullahi cewa "ka yi haƙuri kaman yanda manzannin da suka gabata kamun kai suka yi" bawai Annabi baya haƙurin bane, a'a tunatarwa ce Allah ya ke yiwa habibinsa da kansa, sannan muma al'umman Annabi SAW wajaje da dama Allah yana faɗa mana mu yi haƙuri da kuma fa'idan haƙuri, "Allah yana tare da mai haƙuri (innallaha ma'assabirin), Allah yana son mai haƙuri(innallaha yuhibbul sabirin)...." Wajaje da yawa dai, har ma akwai inda ya ke faɗin, "wa jaza hum bima sabaru jannatan wa hareerah", Banafsha mai haƙuri baya taɓa faɗuwa domin hali ne da Allah ya ke so kuma yake horar da bawa akan ya yi halin." Ajiyan zuciya Umaima ta sauƙe, sannan ta riƙo hannayen Banafsha ta cigaba da magana, "Banafshaty bayan wannan a cikin shika-shikan Imani guda 6, wanda yake na shida a rukuni kuma na qarshen shi ne IMANI DA ƘADDARA WALAU KAIRUN WALAU SHARRUN, kaman yanda ya faɗa a aya ta farko a cikin TABARAKHALLAZHI BI YADIHIL MULKU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN ƘADIR, wannan kalma ta ƙarshe a ayar to tana nufin ƙaddara ce da kuma jarabawan Allah akan bawansa, inason ki sani Banafsha, rayuwanmu gaba-ɗaya akan jarrabawa da kuma ƙaddara take tafiya har mu riske ramin kabarinmu, a cikin SURATUL MULK aya ta 2 Allah subhanahu wata'ala yace :- [Al-Mulk, Verse 2] ألذى خلق الموت والحياة ليبلوكم ايكم احسن عملا و هو العزيز الغفور Allah ya halicci Rayuwa da kuma mutuwa dan ya jarabce mu, a cikin wannan rayuwa akwai abubuwa da yawa waɗanda ya ɓoyesu akan gaibu gare mu, dan sanin su ba ƙaramin masifa bane gare mu, akwai farinciki kuma akwai baƙin ciki, akwai aure kuma akwai mutuwan aure ko rashin aure, akwai samu kuma akwai rashi, akwai haihuwa kuma akwai rashin haihuwan, abubuwa da yawa da Allah ya halitto su yayo kishiyoyinsu dan jarabtar mu, kaman dai yanda yayi mace Nana Hauwa'u kuma yayo namiji Annabi Adamu AS, a wannan lokacin kuma ya sanya wa Annabi Adamu AS kwaɗaituwar keɓancewa da Nana Hauwa'u, wannan ma jarabawa ne tsakanin mace da namiji, Acikin mutuwa kuma Allah yayi jarabawa da yawa wanda shi ma duk imaninka zai jarabce ka, akwai zafin fitan rai, akwai kwanciyan kabari, akwai tambayan kabari, akwai tashuwa bayan Mala'ika Israfil ya busa ƙaho, akwai tsayuwan hisabi, akwai bawa Kowa littafinsa, akwai duba ayyukan kowa, akwai hawa siraɗi da dai sauransu, abubuwa da yawa dan mu sani mu gaba ɗaya a kewaye muke da jarabawa, har sai munyi haƙuri mun kuma aikata dai-dai tare da ƙaunar Manzon Allah SAW, in muka shiga aljanna nan kuma sai Allah da kansa yace ga gidan da ya mana sakamako na haƙurin da muka yi da jarabobin sa akanmu, to sai fa nan ne ba jarrabawa in an shiga aljanna dan kuwa magana ta ƙare, tunda idan aka shiga aljanna ba wani abu da za'a yi mai siga da ibada, to jarabawar da Allah ke jarabtar mu da shi ai idan muka yi haƙuri duk cikin ibada ne, ki amshi ƙaddaranki hannu bibbiyu masoyiya, Banafshaty ba ta inda Allah baya jarabtan bawan sa, wani akan mahaifa, wani akan 'ya'ya, wani akan matan auren sa, wani akan kasuwancin sa, wani ciwo, wani kuma Allah ya bawa wani bawansa daman yin mugun nufi akan ɗayan bawan dan jarabtan su dukan su biyun, wani kuma akan maƙwabtansa, wani kuma akan abokanansa..etc Duk wanda bai yarda da abu biyunnan ba, waɗanda ke ƙidaye a sharruɗan Addini da kuma Imani, to kina tunanin ya cika musulmi kuma mai son Rahamar Ubangiji? Banafshaty wannan ita ce jarabawan ki kuma ƙaddaranki, sannan haƙurin da zaki yi shi ne Zakkan ki, a ko da yaushe kalman haƙuri ita ce kowa zai faɗa miki dan kuwa ansan kina kan stakiyan dandamalin gadon jarabawa, kuma duk wanda aka cewa KAYI/KIYI HAƘURI to tabbas ki sani wannan bawan Allah ko baiwar Allahn ansan ya/ta taka wuta, yanda haƙuri ke kai mu aljanna to haka tun a duniya haƙuri ke kai mu stibirin farin ciki da ɗimbin nasarori wanda bamu taɓa zato ko tsammani ba a rayuwa. Duk wanda ya faɗa miki wata kalma a rayuwanki bayan kiyi haƙuri da kuma ki ci gaba da addu'a, to ki binciki wannan wanda ya faɗa miki kalma saɓanin biyun nan, dan kuwa baya miki kwaɗayin shiga rahamar Ubangiji, ya tabbata ba mai sonki da ƙaunarki ba, domin kuwa addu'a da haƙuri sun isa su miki maganin ko wacce iriyar jarabawa ta rayuwa, duk tsanani yana tare da sauƙi muddin ba wai ka riske makwancinka a wannan halin ba ne, kuma ko da ka riske makwancinka a wannan halin jarabawan bai wuce ba, to shi ɗin ma wani babban nasara ne dan baka san abinda Allah ya shirya maka ba idan ka koma gare sa. Banafsha ki dage da addu'a, duk da dai na sani kina yi, amma ki ƙara dagewa kuma ki duƙufa sosai ki kai kukanki ga mahaliccinki, musamman cikin sujjadanki, a wajan kina tasbihi ga Allah tasbihi ne na yabo, kuma babu mai son yabo irin Allah, kina tasbihinki ki karanto kukanki Insha Allahu komin nisan rayuwa Allah zai amsa miki, don babu inda bawa ya fi kusanci da mahaliccinsa irin sujjada, dan haka ki dage sosai, in Allah ya hukunta ya yarje ya ƙiramu ɗakinsa mai starki sai mu baje dukkan tulin addu'oenmu ga mai amsawa, in kuma Allah bai nufa ba, to daga nan ɗin ma Alhamdulillahi, don kuwa muddim bawa zai tsarkake zuciyansa da jikinsa sannan ya tunkari mahaliccinsa da buƙata, to ko da kuwa a kwance a gadonsa yayi wannan addu'an Insha Allah sai Ubangiji ya amsa, kiyi haƙuri Banafshaty komai zai wuce kuma zai zama labari kaman ba'a yi ba. Batun ki shiga duniya ma wannan butulci ne da kuma rashin nuna amincewa da ƙaddaran Allah, dan kuwa na tabbata duk iya yawan starewanki da kamewanki muddin kika shiga duniya to abinda kika tsana kika sa damuwa a ranki dan shi tom ke ma shi za ki jarabtu da shi ko da kuwa bakya so ne, mutanen duniya ba duka ne na kirki ba, kuma ko da kika ce za ki kashe kanki, to ki sani wannan ya fi komai muni dan kuwa duk storon Allahnki, Addininki, iliminki, soyayyan ki ga Manzon Allah SAW, to duk sun tafi a iska domin duk wanda ya kashe kansa to ya mutu kafiri, wanda direct makomansa wuta ne, mu kuma bamu fatan hakan, muna al'umman Annabi SAW wuta ba namu bane, dan girman Allah Banafshaty kiyi haƙuri ki kuma ƙara haƙuri ki duba maganana kin ji masoyiya" Umaima ta gama maganan tana hawaye. Jikinane yayi mugun sanyi, dan zuwa yanzu ko banu komai to naji sassauci da kuma sanyi a zuciya ta fiye da tunanin mai tunani, kukan ma na neme shi na rasa, dan kuwa duk abinda na sani ƙawata Umaima ta tunatar da ni wanda dama Allah subhanahu wata'ala yace:- **Ka tunatar domin tunatar wa yana amfanan mumini** Ajiyan zuciya na sauƙe na dubi Umaima cikin ƙaunanta da naji ya ninku a zuciyata na ce, "Nagode sosai Umaima, Allah ya saka miki da alheri, Allah ya kuma bar mu tare, in Allah ya yarda zan yi haƙuri, zan ci gaba da addu'a, kuma zan rungumi ƙaddarata hannu bibbiyu domin kuwa kasancewa '𝗬𝗔𝗥 𝗞𝗔𝗥𝗨𝗪𝗔 shi ne babban ƙaddaranta, Alhamdulillahi! Na gode Allah na yabi Annabi, kuma na amsa ƙaddarata Insha Allahu ya Rabbi. Murmushi na sakar wa Umaima na ce, "Masoyiya Umaima dole na dage da karatun musabaƙan nan, dan nima ina kwaɗaice da zuwa ƙasa mai tsarki, mahaifina tun da nake ba'a taɓa bani labarin sa ba sai kawai ni marainiya ce abinda Mami ke faɗamun kenan, ga shi yau har an buɗe baki ance mun ƴar cikin shege, bayan sunan ƴar karuwa, to Alhamdulillahi ni dai ina yiwa mahaifina addu'a, amma ina da buƙatan ƙarawa in ba shi da rai Allah ya masa rahama, idan kuma yana raye to Allah ya haɗa fuskokinmu ko da kuwa gaskiya ne ba ta hanyan halal aka same ni ba, to na yafe musu Duniya da lahira Allah ya yafe mu duka. Ƙiran sallahn Magrib da aka yi shi ya kaste mu muka miƙe duka muka ɗauro alwala muka koma ciki muka bi masallaci sallah, Ummu na ganinmu taji sanyi a ranta ganin damuwan dake kwance a fiska na ya dai-daita. Muna idar da Sallah Umaima ta miƙe ta fice, ni kuma karatun Alkur'ani nake yi har dai aka ƙira isha'i, Umaima ta shigo muka ƙara gabatar wa muna idar wa muka yi lazumin mu muka shafa addu'a sannan muka fito duka. Ummu ta ce, "yauwá yaran albarka ga abinci nan ku zauna kuci ko." Zama muka yi muna ci muna kallo, duk da dai nikam hannu kawai na saka dan kar Ummu tayi magana, amma Umaima duk tana sane da abinda nake yi, sanin halinane na rashin cin abinci ya sanya bata ce mun kala ba. Can muna zaune sai ga kuma sallaman Abba da Umma sun shigo, wani irin bugawa zuciyata tayi da na tuna halin Umma Sabeera ga kuma ya Danish a gida. *** INA KUKE MASU SANA'A, SANA'A MAGANIN TAQAICIN RAYUWA. SAUQI YAZO MUKU HAR INDA KUKE DOMIN WANNAN BA IRIN NA SAURAN BANE Ga mai buqata a tallata masa hajar sa ko kuwa dai sana'ar sa to yai maza ya garzayo ga uwar batoorl mai tallata haja, a rahusa mai sauƙi domin kuwa har da alakoro ina yi. KU TUNTUƁE NI A WANNAN LAYIN NAWA 09161720046 WHATSAPP TELEGRAM 07015870735 WhatsApp ko call Ko Gmail nawa yarmalam96@gmail.com Akan rahusa mai sauqin gaske, sai kunzooooooo🤝 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Dr seeyath (besty lurv) Heartbeat (ukhtynh) Deejatou na Marubuciyar sarauniyar kyau. اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤 🅿️ 21 _ 25 Lumshe idanuwana nayi, muka haɗa baki duka wajan amsa sallaman su Abbaa. Nana dake zaune a gefena tashuwa tayi da gudu ta nufi wajan Abba ta rungume sa tana faɗin, "Sannu da dawowa Abba na." Abbaa murmushi yayi ya ce, "Yauwá maman Abbaa sannunku ko", mayar da kallonsa yayi kan mu ni da Umaima ya ce, "Ummul-khultum da Faɗimah babu yiwa Abbaa oyoyo ko? Yanzu kam yarana sun girma sun zama budurwaye, an daina mini oyoyo" ya faɗa yana sakar mana murmushi. Cikin jin kunya nayi ƙasa da kai na ina murmushi, Umaima ma murmushin tayi muka haɗa baki wajan cewa, "Abbaa sannu da dawowa." "Yauwá ƴan biyun Abbaa, ƴan albarka sannunku ko." Ummu idanuwanta akan mijinta ta ce, "Alhaji in dai ka biye musu ba za ka huta ba fa." Murmusawa Abbaa yayi, ya miƙe ya nufi ɗakin Ummu ita ma ta tashi ta mara masa baya, Umma Sabeera taɓe baki tayi ta bi Ummu da kallon banza, sannan ta juyo kanmu, amma kamun tayi magana muka haɗa baki har da Nana muka ce, "Umma sannu da dawowa." Umma wani dogon tsaki ta ja ta ce, "mstwwww! Iyayen kalen dangi, Allah ya rufamin asiri na zama uwarki tun da dai ni ba karuwa ba ce" ta ƙarishe maganan kaman tana yi da sa'arta ba sa'ar ƴar cikinta ba. Ni kuma a take naji raina ya ɓaci, sai naji gidan ya gundure ni ma, miƙewa nayi zan fice ba tare da na kuma yin ko tari ba, sai Umaima ta tashi ta riƙo hannuna kamun ta buɗe baki ta yi magana, Umma ta rigata ta ce, "Umaima kika kuskura kika ƙara taka ƙafanki kin ji waallahi to sai nayi mugun saɓa miki, shashasha kawai mara zuciya." Umaima tura baki ta yi, da yake shagwaɓaɓɓiya ce sosai har da ɗan buga ƙafanta ta ce, "Masoyiya kiyi haƙuri kinji, ki dawo mu zauna." Kallonta nayi da idanuwana da har sun tara ƙwalla na ce, "A'a Umaima, ki ji maganan Umma, nima gida zan tafi dare tayi", ina gama faɗan haka na juya ina danne hawayena. Umaima biyo ni tayi ban sani ba, muna zuwa dai-dai bakin ƙofa kawai na ji sauƙan mari, ina ɗagowa naga Umaima ta dafe fiskanta, cikin ranaza duka muka kalli wanda ya mare ta, ashe ya Danish tare da su Umma ya shigo, duk abinda ya faru akan idonsa, daman yana staye a bakin ƙofan yana jin mu, haushinsa da tausayin Umaima ne ya rufe ni, na ƙwace hannuna a riƙon da Umaima ta mini, na fice da gudu dan muddin na staya to zan iya ramawa Umaima ko da kuwa kashe ni Ya Danish zai yi. Umma tsaki taja ta ce, "Ka mini dai-dai Danish, Allah ya maka albarka, ke kuma dan ubanki wuce ciki tun da ita ba ƙanwar uwarki ba ce, munafukan yarinya sai liƙewa ƴar karuwa mara tarbiyya take yi, dan son zubarwa mutane mutunci, shashashar yarinya kawai." Da gudu Umaima ta wuce ɗakinsu tana kuka, Umma ganin ya Danish ya fice sai ta wuce nata ɗakin ita ma, tana hararan ɗakin Ummu. Ya Danish kuwa ashe bin bayana yayi, amma ya tarar na jima da shigewa gidanmu, sai guntun tsakin da yaja ya ce, "Wallahi da na kama ki cikin daren nan zan gwada miki digiri na a iskanci, ni ɗin babban ɗan iska ne, amma babu komai, muddin kura na yawo zabo na yawo to watarana za'a haɗu, sai na tabbatar na gyara miki zama." Ina shiga gidanmu na share hawayena na kuma seta kai na, ba tare da na ƙarewa palourn kallo ba na wuce cikin ɗakina, dan bana ƙaunar ƙara wani mummunan ganin irin na ɗazu. Washegari da ya kama asabar da sassafe na gama duk ayyukan da zan yi, ganin Mami bata fito ba cikin taƙaici na fice a gidan ban tunkari ɗakinta ba, dan nasan rashin fitowan ta ba zai wuce tana tare da yaron da na gansu tare jiya ba. Ina fitowa na nufi gidan su Umaima dan mu wuce Tahfiz, amma sai na haɗu da Abbaa a ƙofa yana ƙoƙarin fitowa, ganinsa sai na tsugunna na ce, "Ina kwana Abbaa." Abba na murmushi ya ce, "lafiya Alhamdulillahi Faɗimah, ina kika tsaya haka baki tafi makaranta ba har yanzu?" "Uhmm! Abbaa na tsaya aiki ne, kuma na biyowa Umaima mu tafi tare ne." Abbaa murmushi yayi ya ce, "Ai Ummul-khultum ta jima a makaranta Faɗima, ina ji Mamana ma yanzu ta fitaba jimawa." Miƙewa nayi na ce, "To Abbaa sai mun dawo." "A dawo lafiya Faɗima, Allah ya taimaka ya ba da sa'a." Da "Ameen" na amsa na wuce cikin sauri, dan ina storon dukan latti. Ban bi kan kwalta ba sai nabi ta cikin anguwa duk da kuwa nasan da sassafen nan kam iyayen sa ido basu zauna ba, tunda tukunna yanzu safiya ne, ina isa makaranta na hangi Nana tana shiga ajinsu, nima ajinmu na wuce na shiga da sallama inda na tarar ko malam bai shigo ba, hamdala nayi sannan na nufi kujeran da muke zama da Umaima na samawa kai na mazauni, na dubi Umaima na ce, "Sabahul khair ya Aminiyaty." Murmushi tayi ta rungumeni ta ce, "Masoyiya yau kuma ƴar larabci ne tun malam bai shigo ba?" "Na'am yau larabce malam za muyi, me yasa kika taho kika barni amma?" Na faɗa ina hararanta da manyan idanuwa na. "Banafshaty wallahi ke dai kin sani, labarin gizo ba ya wuce na ƙoƙi, in dai ya Danish na gari to fa sai dai haƙuri za muyi, Umma ce ta sanya ya sako ni gaba dan kar na biya miki, to da muka zo gada ya juya nima sai na juya aikam muka ci karo da shi, nan ya rakoni a guje na ƙariso har cikin makarantar nan" faɗin Umaima tana tura baki kaman ya Danish ɗin ko Umma wani yana kallonta. Na buɗe baki zan yi magana sai malam ya shigo, nan muka dinga gaishe sa shi cikin harshen larabci shima yana amsa mana da larabcin. Malam Abbo nan ya sa muka yi muraja'a aka fara karɓan hadda, kusan sai da rabin ajin suka bada hadda kamun aka iso kan mu, Umaima ce ta fara rero nata karatun cikin zazzaƙar muryanta har ta idar ita ma ba ɓata ko ɗaya, sai kabbara kawai ake yi, tana gamawa malam ya dube ni ya ce, "Bismillah malama Faɗimah Sufyan." Sanin idan an ƙira sunan mutum an iso kan sa kenan, sai na gyara zama na nayi ƙasa da kai na, na fara rero haddan Suratul Taubah, karatu nake cikin muryana mai sanyawa mai sauraro nistuwa inda ba iya ƴan ajin ba hatta Malamin namu in dai zan yi karatu to idanuwan sa na kai na, sai da na kai ayaa sannan na share hawayen dake idanuwana dan ayoyin cikin Suratul Taubah in kasan fassaran su to dole jikinka yayi sanyi duk da wani sashin nata akan kafirai masu munafurtan Addinin Allah suke, wani gefen kuma akan yaƙin Manzon Allah SAW ne. Malam Abbo har nayi shiru idanuwan sa na kaina, sannan ya cigaba da ƙiran sunan sauran ana bada hadda har dai muka gama karatun. Bayan ya ƙara mana mun maimaita sai ya fita, nan malamin Tauhidi ya shigo, bayan ya fita shi ma malamin da ke ɗaukan mu Hadith ya shigo. Tun ƙarfe 6:30am da muka je makaranta mu ne ba'a tashemu ba sai ƙarfe 10:30am. Ana tashi ni da Umaima sai bamu tafi ba muka nufi office na Malam Abbo, sallama muka yi da neman izinin shiga sannan ya umurce mu da mu shigo, durƙusawa muka yi duka, amma sai ya mana nuni da kujera nan muka zauna, sai da ya gama haɗa litattafan gabansa kamun ya ɗago ya kallemu, da larabci ya ce, "lafia kuwa?" Ƙasa nayi da kai na sannan na fara koro masa bayani akan musabaƙa, kallona yayi ya ce, "Faɗimah ai kun makara sai dai na gaba kuma, tun farko kun nuna ba za kuyi ba wanda dama dan na saka baki shiyasa aka barku a makarantar ba'a kore ku ba, sai dai ku bari na wani shekaran, domin waɗanda suka yi yanzu, su za'a je na gari da gari da su." Marairaice wa nayi kaman zan yi kuka, nan muka dinga basa haƙuri, dan munsan Malam Abbo in yayi magana dole a saka mu a masu yi, ba wani babba ba ne shi amma kuma ana ji da shi a malaman makarantan saboda iliminsa, numfasawa yayi ya ce, "Shikkenan zan yi iya ƙoƙarina naga anyi da ku in Allah ya yarda, amma fa sai kun ƙara dagewa da muraja'a, dan an jima da yin nisa a karatun da ya shafi musabaƙan, muddin kuna buƙatan a yi da ku to sai kun dage dan a maye gurbin waɗanda ba sa mayar da hankali da ku." Nan muka dinga godiya muka tabbatar masa da in Allah ya yarda za mu dage, ba za mu basa kunya ba, sannan ya sallamemu muka tashi muka fito a office ɗin, gaba ɗaya makarantar muka bari muna farin ciki dan duk mun saka rai akan wannan musabaƙa, sai addu'a muke kwarara wa malam Abbo. Malam Abbo bin bayan su yayi da kallo yana murmushi, dan ya rasa dalili baya iya yiwa wannan yarinya musu in za ta faɗi abu ko kuma idan abu ya shafe ta..., shigowan wani Malami ne ya dakatar da shi daga tunanin da yake yi, yana murmushi. Zama a kujeran dake kallon sa matashin malamin yayi ya ce, "Haydar na fa raba ka da maganan yarinyar nan, kasan dai wacece mahaifiyar ta da kuma sana'ar ta ko?" Malam Abbo na murmushi ya ce, "Zubair ko me na ce maka ba zaka fahimta ba, amma ina tausayin yarinyar nan akan jarabawan rayuwa da suke ciki da mahaifiyar ta, kuma tsakani da Allah da aure nake ƙaunar ta, sai dai a yanzu tana ɗalibata banjin zan iya furta mata, amma in Allah ya yarda muna yaye su tunda ba zai wuce shekara guda ba zan bayyana mata komai a yi bikinmu akan lokaci da yardan Allah." "Hmmn! haydar kenan, kana tunanin wannan yarinya ta dace da zamowa uwa ga yaranka? Kasan fa ance zina bashi ce to baka tunanin laifin kaka ya shafi jikokinta?" Malam Abbo hallau murmushin ya kuma yi ya ce, "Zubair ina sonta, ina ƙaunarta a haka, kuma in Allah ya yarda ba wannan abu da kake fata, ita ma mahaifiyar nata Allah ya dai-daita al'amuranta ya shirya ta, in Allah yasa Faɗimah rabon Aliyu haidar ce, kuma alkairi gare ni to Allah Ubangiji ya mallaka mini ita, ya rabamu da sharrin masu sharri da masu mugayen magana irinka" ya ƙarishe maganan yana mai da kansa kan takardun gabansa yana murmushi. Malam Zubair taɓe baki yayi ya ce, "kayi nisa baka jin ƙira, kuma koma menene kai za ka jiyo." "Sosaima in dai akan soyayyan Faɗimah-batoola ne, to bana jin komai ba ma iya ƙira ba, ban da mastala da Ummi da kuma Malam duk nasan za su amince dan haka ma na fasa sai ta kammala makaranta, dan a bari ya huce shi yake kawo rabon wani, dan haka ana kammala musabaƙa zan fito da buƙatata in Allah ya yarda, kuma Insha Allahu zan samu karɓuwa." Malam Zubair miƙewa yayi ya fice a office ɗin bai ce komai ba dan yana cike da haushin abokin nasa da ya kasa fahimtar sa. Malam Abbo kuma cigaba da dudduba takardun yayi, dan yana azumin kamawan sabon watan musulunci dan haka sai yamma zai koma yayi wanka ya dawo kamun ɗalibai sun zo tunda ranar weekend safe da yamma ne makarantan nasu. Cikin farinciki Umaima da Banafsha ke tafiya, Umaima ta ce, "heehuhuuu! wa ya ga su Ummu-khultum ɗin Abbaa an zama Hajiya, hhhh! Hajiya Umaima sama, Hajiya Umaima ƙasa, ai wallahi kullum cikin dariya nake dan haƙori yayi ta qyalli, ga mu da wushirya dukanmu, ya kika hango mu masoyiya?" Murmushi nayi na ce, "Kai Umaima kin cika zumuɗi wallahi, yanzu in bamu samu ba fa?" Ɓata fiska Umaima tayi ta harareni ta ce, "Kai amma masoyiya a'uzubillah da wannan mugun fatan, ai in Allah ya yarda mu ne za mu cinye, dan haka in Allah ya yarda zuwa Makka very soon, Madinatul Munawwara is loading." Kallonta nayi na ce, "Amma kinsan wannan na iya cikin Mubi ne ko? Ba lallai mu samu kujera ba, dama dai na jiha da jiha ne ko kuwa ƙasa da ƙasa, wannan kam in Allah ya yarda za'a samu." Murmushi Umaima tamun ta ce, "koma dai menene in Allah ya yarda mun kusa zuwa Makka...." Maganan dake bakinta ne ya maƙale sakamakon abinda muka ji ana faɗa a bayanmu. ''ƳAR KARUWA ! Woooo!! 'YAR KARUWA!!! mai kyawun ɗan maciji, asa hijabi kaman musulman ƙwarai a je makaranta da najasa a jiki, ake ɗaukan Qur'ani wa ma ya sani ko malaman ma raba musu majalisar ake yi, 'YAR KARUWA!! WOOOO!!!!" Cikin taƙaici muka juyo dukanmu ni da Umaima, murmushin da yafi kuka ciwo ne ya ƙwacemini ganin Garba ne ke maganan kuma ga yara kusan uku a gefen sa yana sanya su faɗin ƴar karuwa, suna taya shi yin haukan nasa wanda a tunaninsa yayi dan ya ƙuntata mini ne, bai san yayi a banza ba domin a yanzu ina jin zan iya danne zuciyata ko ma me za'a ce mini, saboda sosai na ji faɗan da Umaima ta mini. Umaima za tayi magana sai na yi saurin taran numfashinta na ce, "Umaima ki ƙyale sa da ƙaramin haukansa, dan ina fara magana ko kuwa kika tanka masa to wallahi sai na kwaɗa masa mari, kinsan halina, muje kawai ki ƙyale sa." Hannunta na kama muka ci gaba da tafiya ina mata hira kaman ba abinda ke damu na amma ita kuma kana ganinta kasan ta sanya abun a rai, ni ake yiwa isgilin amma ita yake damu, Umaima tawa kenan, ina mugun ƙaunarta. Tun daga nesa da muka hango ya Danish tare da abokin sa na yi gefe, ganin bai ganmu ba sai nayi saurin sake hannunta tayi gaba ina bin bayanta ina magana kaman taƙi kulani, saboda kada na ja mata faɗa duk da sai da na lallaɓata, sannan ta yarda da hakan, ina binta a baya ina cewa, "haba Umaima me yasa ba zaki staya mu tafi tare ba? Yau duk kin ƙi kula ni me na miki ne wai?" Har muka isa wajan da yake staye da abokinsa abinda nake faɗa kenan kuma da ƙarfi yanda zai iya jiyo mu, Umaima da ke ƙunshe dariyanta, tana wuce su ta shige gida tana dariya har da kama ciki, idanuwansu duka biyu na kai na har na iso dai-dai su ina magana, na nufi hanyan gidansu Umaima zan shiga sai ya sakarmun wani gigitaccen stawa ya ce, "Keeeeeeeeeeeeeee...! Kar ki sake ki shigar mana gida, tunda kuna da naku ɓace mana a gaban gida." Murmushi nayi wanda ya kawar da damuwan dake raina sannan na juyo na tako har inda suke dan dama ina da cikin sa, stayawa nayi a gabansa ba tare da na kalli abokin sa ba na ce, "Mai digiri a iskanci tun da ba gidan ubanka kai kaɗai bane sai na shiga, kuma Allah ya sa ma muma muna da gidan kai ma ka sani, mtswwww!", Juyawa nayi na shige gidansu Umaima hankalina kwance, rai na fess na ci masa mutunci a gaban abokinsa, shi ma yaji idan da daɗi. Rai a mugun ɓace ya juya zai biyo ni amma ganin Abbaa sai ya fasa ya tsaya yana huci, ni kuwa ganin bai biyo ni ba ko da na leƙo naga Abbaa na ƙofan ai cikin sauri na fito na wuce gidanmu dan dama na riga na gaishe da Abbaa, kuma dan nasan Abbaa na gida shiyasa na masa haka, saboda ba zai taɓa bari ya taɓa ni ba. Abokinsa yana dariyan abinda ya faru ya ce, "Danish wacece yarinyar nan haka?" Ya Danish wani mugun staki ya ja, cikin taƙaici da haushina ya ce, "Mtsww! Dauda ka yi shiru kar ka tambayeni komai, Hmmn! Har ni yarinyar nan za ta dage da qira ɗan iska bayan ga ta cikakkiya tunda uwarta karuwa ce, to wallahi ni nasan abinda zan mata" ya Danish kaman zai daki babu haka ya dinga huci, abokinsa sai dariya ya ke, shi kuma duk ya bi ya cika yayi fam kaɗan yake jira ya fashe. Mun yi hutun weekend cikin kwanciyar hankali da farincikin kasancewanmj cikin masu musabaƙa, dan kuwa Malam Abbo (haydar) ya tsaya mana komai da mu ake damawa, taƙaicin rayuwa kuwa ba abinda ya ragu sai ma ƙaruwa dan bazan fita na dawo gida ba tare da an jefe ni da mugun magana ba, tsakanina da ya Danish kuwa ba komai sai tarin stana da kuma burin quntatawa juna bai ƙyaleni ba, nima ban ƙyalesa ba, ba ya tausayina ni kuma bana storonsa ko zai kashe ni sai na masa abinda na ga dama. Yau da yake Monday muka shirya muka tafi makaranta, bayan mun gama class bayan azahar muka dawo ba hutu muka shirya 4:00pm muka tafi Tahfiz, mu ne bamu dawo ba sai 6:30, muna dawowa Umaima ta shige gidansu, nima nayi namu dan kuwa yau ya Danish baya gari dama daga juma'a zuwa Lahadi kaɗai ake ganinsa a gida. Bayan wata guda abubuwa sun taru sun mini yamun yawa, yanzu ya zamana ma banda lokacin yawan yin tunani ko kuka dan kuwa exam's ne a gabanmu na fita aji biyu a makaranta, sannan ga musabaƙa ya zo shi ma saura sati biyu, exam's kuma Monday mai zuwa za mu fara wanda yau yake Thursday, Allah ya so dai a satin da muka gama exam's,sati mai kamawa shi ne na musabaƙan. Zaune nake a palourn mu daga ni sai under-wear da vest na baza hangout a gaba na ina kan duba wa, kai na ba ɗan kwali kiston ebra da Umaima ta mini manya da qanana jelar har kusan ƙugu na, ba tare da naji sallama ko mosti ba kawai naji hannun mutum a kai na yana jan jelar gashi na, ɓata fiska nayi na ɗago dan duk a tunanina Umaima ce za faɗa mata bana so, domin nasan ita ce mayyar gashina idan tamin kisto sai ta dinga damuna kenan sai na kulle kai na nake hutawa, maganan dake baki nane ya maƙale ganin wani babban dattijo da shirgegen ƙaton cikinsa yana washe mini bakin da na tabbata haƙoransa sauran babu, yana murmushin da ke ƙara masa muni ya ce, "Yarinya kin yi kyau ƴar shila da ke haka." Cikin taƙaici na miƙe na ɗaga hannu da niyan kwaɗa masa mari, sai kuma na tuna babban mutum ne ya yi jika da ni ma ba ƴa ba, ƙwafa nayi tare da jefansa da mugun kallo na tsana na ce "Stohon banza da wofi wanda bai san daraja da mutuncin ƴa mace ba, kai dube ka fa sa'an kaka na kana wani washemun shaddan bakinka stohon najadu kawai, wallahi ka ci albarkacin musulunci da stufan ka, da abinda zan maka ba za ka iya ɗauka ba", ina gama magana na rarumi hijab nawa na saka, na sunkuya ina tattara takaddu na. Muryansa na ƙara stinkayowa yana cewa, "Haba ƴar shilah ai kyawunki ne ya ja kuma bar ƙira na da stoho, nan da kika ganni sai na miki abinda yaro ɗan shekara 30 ba zai miki ba domin kuwa kayan aikin da ƙarfinsu ko mamarki bata sharewa a buga wasa da ni." Ɗagowa nayi idanuwa har sun kaɗa dan baqin ciki da taƙaicin maganansa na ce, "Wallahi idan har kana da kunya to kaji kunya, kuma ka yi asara dan daka ganni nan nafi ƙarfin ka kuma uwata ma daga yau ina tabbatar maka ba kai ba ita" na faɗa ina wucewa ɗakina tare da banko ƙofana. Ina cire hijab na zube kan gado ina jin kuka nason ƙwace mini, sai kawai naga mutum ya shigo min ɗaki daga shi sai boxer da vest, tashuwa nayi a storace cikin in'ina na ce, "kaa kaaa, memm... me.. ya kawo ka ɗaki naa?" Na faɗa murya na rawa ganin stoho ba kaya ga kuma wani abu da nake hangowa a wandon sa ya miƙe kaman katako aka sanya masa a cikin wando. Kai na ya iyo yana washe baki, kamun na buɗe baki da niyan lwala ihu na ji muryan Mami na cikin mugun stawa ta ce, "Alhaji sabooooo! Yarinyar tawa za ka ƙetawa mutunci a gidana?" Cikin razana stohon ya juya yana rarraba ido ganin Mamina, ai da gudu nayi wajanta na ɓoye a bayanta ina sakin marayan kuka, rungumeni tayi taja hannuna muka fice a ɗakin ta yafamun mayafin jikinta, ba tare da ta ce mini ko ƙala ba. Muna zaune a palourn sai stohon ya fito yana sussunne kai, ya buɗe baki zai yi magana Mamina ta miƙe ta kifa masa mari, cikin mugun ɓacin rai ta ce, "Kai Sabo mara mutunci, mastiyaci, ɗan iska, stohon da baisan daraja da mutuncin yara ba, ka fice mini a gida tunda bada kuɗin ubanka na gina ba, ko kuwa na ƙira maka hukuma yanzun nan, kai ba hukuma ma ni nan na ishe ka, indai a kan wannan yarinyar tawa ce to zan iya kashe mutum." Stohon nan jin zagin Mami sai ransa ya ɓaci ya ce, "naji ba da kuɗin ubana kika gina ba domin kuɗin ubana yafi ƙarfin ki, kuɗin ubana kuɗin halal ne ke kuma karuwa ce ita kuma ƴar taki da kike tunani tana da mutunci to bata da sauran mutunci, don kuwa ƴar karuwa ce ita, maras mutunci har ni za ki gani ki zaga? To wallahi ba yarinyarki ba aure, kuma ita ma Insha Allahu sai tayi abinda kike yi, sai ta lalace, sai ta yi abinda ma ba ki yi ba tunda kika ɗaura hannunki a jikina saboda ita" ya faɗa yana ficewa a palournmu da kayansa a hannunsa. Cikin kuka nake bin su da ido, shi da Mamina duka har ya fice, Mami zuwa tayi wajena ta zauna, tana ƙoƙarin ɗaura hannunta a jikina na miƙe cikin gaggawa ina kuka na shiga ɗakina da gudu ina kuka mai cin rai, abubawan da ke faruwa ya fara isa ta, bana jin zan iya daurewa, abin da yawa wai shege da hauka, ga shi shege ga shi mahaukaci. *** Ina kyautan page ne ga masu Sharhi yanda ya kamata, da kuma waɗanda ke bada gudumawa a tafiyar wannan littafi, sister ba kya Sharhi kuma kar ki ce ba'a baki page ba, littafi dai yanzu aka fara tukunna ba abinda muka yi, so a dage da Sharhi fan's. Lurv you all # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Ummu muhammad Maman Mhm'd Nana Khadijah Feenah's touch (Allah Ubangiji ya baki lafiya dear)🤲 اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 26 _ 30 A haka na cigaba da risgar kukana, har ɓarawon bacci yayi awun gaba da ni, kuma tun daga wannan ranar ko ƙofan gida ban ƙara fita ba, balle kuma ayi maganan makarantar boko, ko kuma Tahfiz dan wannan abu da ya faru da kalaman mutumin nan ya dame ni ba kaɗan ba, nan dai na dinga salloli kawai ina karatun Alƙur'ani dan samun nistuwa, tsakanina da Mamina sai gaisuwa duk yanda ta so nayi magana naƙi yi, sai dai Umaima idan ta shigo mu yi magana sama-sama ita ma, amma bana iya dogon magana dan kuwa inajin ciwo a rai na, duk abinda ya faru kuwa ko kuka na kasa yi tun ranan alhamis da abun ya faru har yau da yake Lahadi. Yau ma kaman ko yaushe ina cikin ɗakina, ina zaune a kan darduma da Alƙur'ani a hannuna, shigowa Umaima tayi ɗakin da sallama ta same ni da Qur'anin na buɗe na zuba masa ido amma ba karatun nake yi ba, har ta gama sallamanta ban ji ba, sai da ta taɓa ni kamun na ɗago firgit na zuba mata idanuwana da kana ganinsu za ka ga raman da nayi, cikin damuwa ta ce, "Masoyiya mene haka wai? Duk kin bi kin sauya, duba fa har ramewa kike yi, kuma na tambayeki kin ce ba komai, me yasa kike yin haka ne Banafsha? Ko kina so damuwa ya faɗar da Mami ne? Ke kin ƙi zuwa boko kuma kin ƙi zuwa tahfiz, kin sa hankalin Mami ya tashi, yanzu ke hakan ya miki?" Lumshe idanuwana nayi kawai ba tare da na bata amsa ba, tunda na amsa sallaman da ta yi ban ce komai ba, ganin nayi shiru kuma tasan halina idan na yi hakan ba maganan zan yi ba, ko ya za'a yi da ni, sai ta girgiza kai kawai ta ce, "Allah ya kyauta! Idan kin gama shirun naki sai ki fito, Malam Abbo yana palour yana jiranki, kuma ya jima da zuwa." A ɗan razane na buɗe idanuwana na kalleta, na kuma maimaita sunan da ta faɗa "Malam Abbo!", wani nauyayyan ajiyan zuciya na sauƙe wanda bansan nayo sa ba, a zuciyana na ce, "To me ya kawo sa gidanmu?" Muryan Umaima na tsinkayo tana faɗin, "Idan kin fito ai zai faɗa miki abinda ya kawo sa gidanku, ni dai dan Allah ki fito dan ya jima da zuwa", Umaima na gama faɗan haka ta fice a ɗakin. Ni kuma da kallo na bita har ta fice ina mamaki, ashe maganan nawa a fili nayi ba'a zuciya ba, sai kuma gefe guda da nake tunanin abinda ya kawo sa gidanmu a irin wannan lokaci, kuma dai na ga ban wani jima da daina zuwa makarantar ba, share tunanin nayi na miƙe tare da rufe Qur'anin, na ajiye sa a wajan zamansa, ba tare da na tsaya yin komai ba na nufi hanyan palourn tunda daman ƙaton hijabi ne a jiki na, Umaima ta faɗa mini ya jima da zuwa, banson na tsaya ɓata lokaci ya ga kaman na renasa ina ɗalibarsa, kuma nima a maste nake naji abinda ya kawo sa. Da sallama na shigo palourn namu, inda na same sa zaune a ɗaya daga cikin kujerun palourn, cikin shigansa ta alfarma da kamala kaman ko yaushe, Malam Abbo kyakkyawan gaske ne, sanye yake da jamfa dark-green mai ɗinkin da ake kira half-jamfa, da hulansa sannan ƙafan sa har da safa, agogo mai kyau ne a maƙale a hannunsa wanda idan ka gani za ka ɗauka ya kai na dubbanni saboda haɗuwan agogon. Malam Abbo kenan saurayi matashin Malami mai ji da kyau da kuma ilimi boko da Arabic, namiji ne shi har namiji, duk inda ake neman namiji cikakke to ya kai. Asalin sunan sa ALIYU HAIDAR haifaffen cikin garin Mubi ne, inda suke zaune da iyayensa a anguwan kwaccam amma ba kusa da gidajenmu ba, mahaifinsa da mahaifiyarsa duka malamai ne, shi mahaifin nasa limamin masallacin juma'a ne na ƴan shi'a a cikin Mubi. Malam Abbo shi ne ɗan Auta a wajan iyayensa, yana da yayyu maza biyu da yayyu mata biyu, Malam Abbo ba zai wuce shekaru ishirin da shida zuwa da takwas ba, kuma kyakkyawa ne shi na bugawa a jarida, yana da ilimi sosai-sosai a boko ya karanci Islamic Education, yayi har degree biyu, a addini kuma yana da haddan Qur'an mai girma complete a kansa da tafseer nasa da komai, yana da littatafai a kansa ba adadi kuma har yanzun yana kan ƙara karatun ne, domin musabaƙan sa na ƙarshe anɗau nauyin karatunsa da komansa a Madina, kawai bai tafi bane, amma idan ya shirya ko yaushe komai nasa yana nan ready. Cikin nistuwa na samu waje na zauna a ƙasa tare da sunkuyar da kai na, a hankali cike da ladabi na gaishe da Malam Abbo, shi kuma ya amsa mini yana murmushi. Umaima da ke zaune can gefe da ni kaɗan, miƙewa tayi ta ce, "Banafsha na gudu gida Umma ta aike ni." Na ɗago kai zan ma Umaima magana, cikin rashin sa'a na haɗa ido da malam Abbo da ya zuba mini idanuwansa, wani iri naji a jikina nayi saurin yin ƙasa da kai na tare da cewa, "To sai kin dawo, ki gaishe da Ummu." Umaima ficewa tayi bayan ta yiwa Mamina da Malam Abbo sallama, sai da ta fice sannan Malam Abbo ya dubeni ya ce, "tashi a ƙasa Malama Faɗima." Kai na a duƙe ina wasa da yastuna na ce, "Nan ma yayi Malam." Malam Abbo yayi-yayi na koma saman kujera amma naƙi, ganin na dage sai ya ƙyaleni kawai yayi murmushi, tare da gyaran murya ya ce, "Malama faɗima kinga na biyoki har gida ko? Nasan kina mamakin me ya kawo ni ko?" Murmushi kawai na yi kai na a ƙasa har yanzu, kuma ban ce komai ba, dan kuwa gani nayi Malam Abbo kaman ya karance zuciyata ne. Shi kuma ganin murmushin nawa sai hakan ya wadatar da shi amsan da zan buɗe baki na basa, cikin nustuwa ya fara magana, "Malama Faɗima da farko dai zan tambaye ki abinda ya hanaki zuwa makaranta, duk da bai kamata na tambayeki har gida ba, kamata yayi kije makaranta ki faɗa mini dalili, idan ta kama ta hukunci kuma sai na miki, idan na yafiya ne kuma sai na miki afuwa, to yanzu bisa ga wani dalili ga ni har gida, kuma ina tambayarki me ya hanaki zuwa kwana biyu, bayan kinsan akwai maganan musabaƙa da ake staka da shi." Wani nauyayyan ajiyan zuciya na sauƙe jin tambayan Malam Abbo, wanda nasan da shekara za'a yi yana tambayana irin haka, to za'a kwashe wani shekaran nima ban basa amsa ba, balle na faɗa masa gaskiyan abinda ya faru ko ya hanani zuwa makarantar, kuma ga shi dai a rayuwata ni ban iya ƙarya ba, dole shirun dai shi zan yi, saboda wannan sirrinane ni da mahaifiyata, ko Umaima ba zan sanar da ita abinda ya faru ba balle wani a gefe, ban taɓa jin zan iya ɓoye wa Umaima wani abu ba sai wannan lokacin، a hankali na haɗiye wani mugun yawun da ya tokare mini maƙoshi na tuno abinda ya faru ranan, ɗago kai na nayi tare da kallon Malam Abbo, jin hawaye na neman zubo mini sai nayi saurin yin ƙasa da kai na ina haɗiye kukana da hawayena, dan basu da amfani tunda ko yaya za'a yi da ni ba faɗan dalilin zubansu zan yi ba. Malam Abbo daman idanuwansa na kai na, kuma ko da na ɗago kai na idanuwanmu sun haɗu, kuma ina da tabbacin ya hango damuwan da ke cikinsu, ajiyan zuciya ya sauƙe kaman yanda ya ke a nawa ɓangaren, a karo na biyu ya tambaye ni me ya hanani zuwa makaranta, amma nan ɗin ma shirun na masa kawai tare da girgiza kai, ganin haka sai ya jinjina kai dan yana da tabbacin wani abun nake ɓoye masa, ko kuma ba zan iya faɗa masa ba, bai kawo komai a ransa ba kawai ya ce, "To shikkenan na fahimta Malama Faɗima, Allah rufa mana asiri duniya da lahira, Allah ya iya mana a lamuranmu, abu na gaba kuma da zan faɗa wanda shi ne babban dalilin zuwana, maganane akan musabaƙa, kinsan dai halin da ake ciki, ɗalibai masu gabatar da karatun musabaƙa anjima da zaɓansu, amma kuma da kuka same ni da maganan kuna son ku yi, sai na sama muku gurbi tunda makaranta gaba-ɗaya an sheda da irin ƙoƙarin ku da hazaƙan ku, to kina neman kawo tangarɗa a lamarin, ko kuma na ce kin riga da kin kawo, tunda hankalin hukaman makaranta ya dawo kanku, musamman ma dai ke, kuma maganan shiganku jerin masu musabaƙa anyi cancel nashi, kuma saboda rashin zuwanki, hukuman makaranta na batun sallamanki dan kina son basu kunya ko kawo musu wani naƙasu a tafiyansu, na zo ne in sanar da ke abinda ake ciki kuma makaranta ce da kanta ta turo ni, idan ba ki koma akan lokaci ba to komai na iya faruwa, da naso faɗa wa Malama Ummu-khultum ta isar miki da saƙon amma kuma sai makaranta ta bukaci da nazo da kai na." Wani irin bugawa ƙirji na ke yi zufa na ƙeto mini, jin wai an ciremu a masu yin musabaƙa kuma makaranta na son sallamana, mu da muke ƙoƙarin haɗawa a yayemu ba da jimawa ba in Allah ya yarda, kuma dai duk da ba dan abinda zan samu zan yi musabaƙa ba, amma na gama saka wa a raina in Allah ya yarda zan yi nasara, idan Allah ya ƙira mu muka samu zuwa ƙasa mai starki na samu na yi wa mahaifiyata addu'a, ai dole abin ya dame ni, kaman zan yi kuka na ɗago kai na, muryana na rawa na ce, "Malam dan Allah ka yi haƙuri, dan darajan Annabi SAW kada ku cire mu a masu yin musabaƙan.' Malam Abbo ajiyan zuciya ya sauƙe ya kawar da kansa daga kallona ya ce, "Ni dai ban da yacce zan yi kuma a ƙara baku wata daman, wannan ku ne ya kamata ku ƙoƙarta ku samawa kanku wata damar." "Malam duk abinda ya kamata muyi za muyi in Allah ya yarda, amma ku yi haƙuri kada ku cire mu" ma faɗa hawaye na taruwa a idanuwana. Numfasawa yayi ya ce, "To yanzu dai ni shawara guda zan baki, maganan zuwa makaranta duk rinsti duk wuya kada ki ce za ki aje karatu a gefe, ko me ya samu bawa ko kuma ya faru to muƙaddari ne daga Allah, ki dage da karatu sannan kije makaranta, ina tunanin hakan zai sa hukumar makaranta ta fasa abinda ta yi niya, idan aka ga kina zuwa kuma kin dage da karatun, to dole za su buƙaci yin tafiyan da ke." Lumshe idanuwana nayi, hawaye suka gangaro akan kumatuna, ba tare da na goge su ko na hana su gangarowa ba na sauƙe ajiyan zuciya da kuma hamdala, ko babu komai zan ji sanyi a rai na idan nayi hawayen, tun ranan na kasa kuka balle hawaye har yau, kuma zuwa makaranta ya zamo mini dole, sannan dagewa da karatu ya zamo mini dole shi ma, a hankali na buɗe baki da muryana da ke rawa na ce, "Malam zan je makarantar Insha Allah, kuma zan dage sosai, mun gode Allah saka da alkairi." Murmushi Malam Abbo ya saki wanda nima Uwar batoorl bansan na me bane, amma dai da alama da wani abun, cewa yayi, "ki mini magana da Umma zan tafi." Tashuwa nayi na nufi ɗakin Mamina, da sallama na tura ƙofan na shiga, bayan ta amsa mini, na faɗa mata Malaminmu na mata magana zai tafi, Mami ta amsa akan tana zuwa ni kuma na juya na koma palourn, samun Malam Abbo nayi har ya miƙe ma, kallo ɗaya na masa na ɗauke kai na faɗa masa tana zuwa, ban gama rufe baki ba sai ga Mamina ta iso, Malam Abbo durƙusawa yayi yana faɗa wa Mami zai tafi, ni kuma gaba nayi na fice ma a palourn gaba-ɗaya ina yabawa da girmama Mamina da Malam Abbo yayi, sosai naji daɗin yanda yayi ba tare da girman kai ba. Mami ganin na fice a palourn sai ta buƙaci Malam Abbo ya tashi, tashuwa yayi ya zauna ita ma ta zauna, kansa a ƙasa cikin ládabi ya ce, "Umma mun gama magana da Malama Faɗima, kuma nayi duk abinda ya dace wanda nasan zai sa ta dawo normal, Insha Allah ina da tabbacin har makarantar bokon za taje." Mami farinciki kaman tayi yaya, tana murmushi da jinjina ƙoƙarin Malam Abbo ta ce, "Nagode sosai Malam, Allah saka da alkairi, Allah maka albarka, Nagode sosai." Malam Abbo miƙewa yayi bayan sun gana magana ya fice, Mami sai godiya take masa, ta miƙa masa kuɗi ma ya ƙi amsa, a stakar gidan suka same ni staye, Mami ta dubeni ta ce, "Banafsha sai ki takawa malamin naku ko." Amsawa Mami nayi, ita kuma ta juya ta koma cikin gida cike da farin ciki, ko ba komai yanzu 'yar ta za ta saki ranta, ta daina saka damuwa a ranta. Ni kuma kaman yanda Mamina ta faɗa hakan nayi, tare muka fice da Malam Abbo a gidanmu, yana min faɗa, cewa yayi, "Malama Faɗima, komai na rayuwa da kike gani haƙuri ake yi da shi, kuma ƙoƙari ake yi wajan ganin mutum ya cinye jarabawan mahaliccinsa, saboda samun gwaggwaɓan rabo da sakamako mai kyau a duniya da kuma ranan karɓan sakamako, ita kuma jarabawa a zagaye da mu take ko ta ina, a iya karatunki nasan kin sani, ayoyi da dama na ƙur'ani sun kawo hakan, sannan akwai wasu hadisan ma da suka kawo haka, Malama Faɗima hatta rayuwa da kike gani da Allah ya mana ya kuma azurtamu da lafiya to shi ma jarabawa ne, Allah ya jarabce mu da lafiya ne dan ya ga ya za mu yi da lafiyan, aljanna za mu nema da shi ko kuwa za mu dage wajan saɓa masa ne, rashin lafiya ma jarabta ce dan ya ga mutum zai yi haƙuri ya yarda da Allah ne ya ɗaura masa cutan ko kuwa zai dinga zargin mutane akan da saka hannunsu, haka zalika akan dukiya da rashin dukiya, akan haihuwa da rashin haihuwa, akan tashuwa ka rayu da iyayenka da kuma rayuwa ba tare da su ba, haka akan aure da rashin yin aure, komai da yake zagaye da ɗan Adam na jarabta ce daga mahaliccinsa, kuma Allah na so ne mu ci wannan jarabawan, ina fatan kin fahimta kuma za ki dage wajan ganin kema kin cinye naki jarabawan?" Faɗin Malam Abbo da ya dakata da tafiya ya zuba mini idanuwansa dai-dai mun shige ƙofan gidan su Umaima, kuma cikin rashin sa'a sai ga Ya Danish a waje shi da abokinsa kasancewan yau Lahadi yana gida bai koma ba tukunna. Ya Danish yana zaune a bayan motansa, sai abokinsa ɗaya na zaune a plastic chair, da kuma Ya Farooq shima yana zaune a kujeran roba, ya Farooq ɗan farin Ummu ne, kuma kusan sa'a haka suke shi da Ya Danish, shiyasa suke yawan zama tare, muddin Ya Danish na gari to za ka gansu tare da wannan abokin nasu mai suna IB. Ya Danish tun fitowanmu idanuwansa suka sauƙa a cikin nawa, wani irin kallon banza kallon tsana yake jifana da shi, ni kuwa ganin ya zuba mana ido sai na dinga sakarwa Malam Abbo murmushi, har dai muka tsaya ɗan gaba da su kaɗan, wani kallo na yiwa Ya Danish wanda shi kaɗai yasan fassaranshi ta 'yar staman da ke tsakaninmu, sannan na mayar da hankalina kan Malam Abbo ina masa magana, Ya Danish kuwa a nasa ɓangaren wani wawan dogon staki ya ja, wanda sai da Ya Farooq da ya IB suka tambayesa menene, amma ya musu banza. Idanuwana akan malam Abbo ina ƙayataccen murmushi na ce, "in Allah ya yarda Malam zan dage, wajan ganin na cinye tawa jarabawar, sannan na maka alƙawarin dagewa a karatu da zuwa makaranta, nagode sosai Malam, Allah ya biya ka da mafificin alkairi, Allah ya biya iyayenka da aljanna, Allah ya sa ka rabu da su lafiya nagode sosai." Tunda na fara magana Malam Abbo ya zuba mini idanuwansa masu ɗauke da sinadaran da ke saka ni jin kunya, amma duk da haka ban kawar da nawa idon ba sai ma wani murmushin da nake sakar masa, wanda duk saboda Ya Danish na daure nake yin hakan, shi kuwa Malam Abbo tuni ya susuce wajan kallona, inada tabbacin ya tafi wata duniya ta daban, ganin kaman hankalinsa ba ya wajan sai na ɗan mosta yastuna a gaban idanuwansa na ce, "Malam muje ko." Firgit Malam Abbo ya dawo daga duniyan da yake, yana mai dannewa dan kada na fahimta, ganin har yanzu da murmushi akan fiskana sai shi ma ya sakar mini tare da faɗin, "Malama Faɗima rakiyan ya isa haka, ki juya nagode ko." Ba tare da musu ba na gyaɗa kai tare da masa addu'an a koma lafiya na ƙara da godiya, ban juya ba sai da Malam Abbo ya juya ya fara tafiya, na ɗaga masa hannu sannan ganin ya ɓacewa ganina sai na juyo ina ta murmushi ni kaɗai, har na mance da abinda ke damuna domin kuwa nasihan Malam Abbo ya shiga jikina ba kaɗan ba. Ina juyawa kuwa idanuwana karaf a cikin na Ya Danish, wani killer smile na sakar masa tare da cigaba da tafiya na, wannan karon ma ƙwafa Ya Danish yayi, wanda ya sanya su Ya Farooq bin inda yake kallo da idanuwansu, Ya Farooq suna ganin ni ce sai kawai suka yi dariya, daga Ya Farooq har Ya IB sun san za'a rina, Ya Farooq ne ya ƙwala mini ƙira tare da cewa Ya Danish, "Amma dai ka ji jiki wallahi, Allah taro ka Danish, ka saki ranka ka daina haushi da yarinya a banza, ita bata damu da tsabgarka ba amma ka bi ka azalzali yarinya." Ya Danish kallon banza ya yiwa ya Farooq tare da yin ƙwafa, ni kuwa ganin ya Farooq ne ya ƙira ni sai na taho cikin tafiyana ta nistuwa da ɗaukan hankali, har na iso inda suke zaune, ɗan rusunawa nayi na ce, "Ya Farooq ina wuni, Ya IB barka da yamma." Ya Farooq da Ya IB duk amsawa suka yi da murmushi, Ya Farooq ya ce, "Daga ina haka da yamman nan sistor?" Langwaɓar da kai nayi gefe guda tare da kulle idona ina murmushi na ce, "saurayina ne ya zo zance, shi ne na rakasa." Tun kamun na rufe baki ya Danish ya ja wani dogon tsaki, daman shi kaɗai ya ganni basu ganni da saurayin ba, kuma ga haushin na gaida su ban gaishe sa ba saboda na renasa, Ya Farooq ko kallon Ya Danish bai yi ba duk da yasan yayi tsaki, murmushi ya sakar mini ya ce, "inye! Su sistor har an girma an yi saurayi, daman Umaima ta faɗa mini gobe za ku fara exam's, ashe next year ana gama school sai biki kenan?" Rufe fiskana nayi da tafin hannayena sannan na Jinjina kai alaman eh, Ya IB ne yayi dariya ya ce, "Yaran yanzu ba kunya, har da kai kike ɗagawa, shikkenan Allah nuna mana da rai da lafiya, Allah tabbatar da alkairi." Da "Ameen" na amsa ina yin ƙasa da kai na tare da wasa da yastu na, Ya Danish da ya cika ya gama cika, wani banzan tsawa ya mini ya ce, "Keeeeeeeeeeee! Dallah ɓace ma mutane a kai, 'yar iska kawai, shashasha ƙwaila, mara tarbiyya." Duk da storon da stawan nasa ya bani amma hakan bai saka na tafi ba sai da na tsaya na sakar masa wani killer smile ɗin, na kashe masa ido guda na ce, "ai ba'a ɗan iska ɗaya, sai dai biyu, kaga kuwa ni kaɗai ba iya yin iskancin da kai na zan yi ba, dole tare da kai nake yi" Ina gama faɗan haka na juya na shige gidannasu, hankalina kwance. Ya Farooq da Ya IB duk dariya suka kama yi, suna faɗin ai ga abinda suke guje masa kenan, ga shi tun ina storonsa amma ya saka na daina storonsa balle storon faɗa masa magana, na gaishe da kowa amma banda shi, kuma duk shi ya jawo ba kowa ba. A tsakar gidan na haɗu da Umma Sabeera, ɗan rusunawa nayi na gaisheta amma ta aika mini da harara ta ce, "Ke dan uwarki karuwa ki fice mana a gida tunda ba gidan ubanki ba ne.." Kamun ta ƙarisa maganan tuni muryan Abbaa ya dakatar da ita, ta hanyar cewa, "Sabeera ki fita a idanuwana na kulle, ke Faɗima maza zo ki shige inga gidan nawa ne ko nata, idan ta isa ta hana wanda na bari ya shiga gidan." Kai na a ƙasa ba tare da damuwa ko ɗigo a fiskana ba, na gaishe da Abbaa ya amsa, sannan na miƙe na shige gidan ina magana a zuciyata ni ɗaya, ba dan Umma Sabeera na cin albarkacin Umaima da Abbaa ba, ai da tuni ita ma na fara kasa mata hali na tasan banda sauƙi, ni ɗin do me i do you ce, back to back aradu, kana mini ina ramawa ba barin bashi kuma ba ruwana da girmanka. Abbaa ya dubi Umma bayan shigewana ya ce, "Sabeera indai kina da kunya to kin ji shi, ƴar cikinki amma kike mata abu kaman sa'arki, yanzu da ta rama zagin fa? Ƙawar ƴar ki ce fa ba wai babbar mace ba ce, ki gyara halinki idan ba haka ba wallahi za ki sa nayi abinda ban yi niya ba, indai akan mahaifiyarta kike wannan abun, to sai na aure ta naga abinda za ki yi, ko kuwa na zama dadironta na ga ƙarshen rashin tunaninki da rashin hankalinki..." haka Abbaa ya dinga yiwa Umma Sabeera faɗa kaman wanda aka aiko sa da wahayin faɗan, ita kuwa Umma wani irin stanata ne ya ƙara rufeta, tana jin za ta iya kasheni ma akan abinda Abbaa ya faɗa, na ya haɗa alaƙa da Mamina. Ni kuwa ina shigewa ciki na gaishe da Ummu sama-sama, da yake nasan abinda na shuka a waje da wuri na fito na ce Umaima ta zo ta rakani, so nake kamun Abbaa ya fita na gudu gida, idan ta Ya Danish ne banda mastala zan iya tsayuwa mu daku ma, amma kuma Umma ita nake shakka saboda mijinta da 'yar ta, kada ta ce za ta taɓa ni kuma ba iya ƙyalewa zan yi ba. Umaima sai mita take daga zuwana zan tafi, ko labarta mata yanda muka yi da Malam Abbo ban yi ba, haka dai na yafito ta muka fito, Allah ya taimaka lokacin Umma ta shige ɗakin Abbaa da ke ta cikin gidan, hamdala nayi muka nufi waje, muna ficewa a gidan kuwa muka kusa yin karo da Ya Danish, wani mugun kallo ya aikawa Umaima amma ta kawar da kai kaman bata ga ni ba, tsawa ya daka mata da mugun ƙarfi ya ce, "kin juya kin koma gida ne ko sai na iso wajan na ɓaɓɓallaki? Ban hanaki haɗa hanya da yarinyar nan ba?" Kamun mu yi wani mosti sai muka kuma jiyo muryan Abbaa, ashe yana bayanmu bai fita ba, dan-ƙwalo ya aika wa Ya Danish, sannan ya ce, "ke Umaima wuce ku tafi, idan kun je ki kwana a can, sai naga ko akwai wanda ya haifa mini ke, da zai mini iko da yarinya." Fakan idon Abbaa nayi na murguɗa wa ya Danish baki tare da gwalo, na kuma masa magana da ido wanda na tabbata ya fahimci abinda nake nufi, daga kallon da ya mini, jan hannun Umaima nayi muka yi wa Abbaa sai da safe muka wuce gidanmu, shi kuma ya Danish fasa shiga gidan yayi daga wajan ya shige motansa yayi gaba saboda Ya Danish akwai zuciya, Abbaa ma wucews inda zai tafi yayi. Malam Abbo tun da ya juya ya tafi babu abinda yake tinanowa sai murmushin da Banafsha ke sakar masa, da kuma kallon da take masa, tuni ya ƙara matowa a kanta, nan ya ci alwashin ya kusa bayyanar mata da saƙon zuciyarsa. Muna shiga gidanmu Umaima ta dinga dariya kaman ba lafiya ba, kallonta nayi na ce, "an fara sanyi kuma ai, hauka ta fara mostawa." Tana dariyan ta ce, "Masoyiya ba za ki fahimta ba, ni ba haukar ce ta mosta ba, abinda Abbaa yayi ne ya mini sweet, ga shi Ya Danish ya ja an ce na kwana anan, wayyo mi farinciki kashe ni, yau za mu kwana karatu saboda peppernmu na gobe, Allah ya yiwa Ya Danish albarka, Allah ya sa watarana Umma ma tayi a gaban Abbaa, ya ce ya bawa Maminmu ni kyauta, heee!hu!hu!" Hararan Umaima kawai na yi muka shige palourn namu, ban sanar mata abinda ya faru stakanina da Umma ba ɗazu, domin duk son da Umaima ke mini to fa uwa-uwace, kuma wannan ba baƙon abu bane, hantara daga wajan Umma da Ya Danish ba sabo bane a wajena. Da sallama muka shiga palourn amma ba kowa shiru, ɗakina muka wuce direct muka yi alwala tare da yin sallah, mun idar muka fito palour muka samu Mamina zaune tana cin abinci, ganina da Umaima bata yi mamaki ba, kuma bata tambaya ba, domin ba wannan ne karo na farko da Umaima ke kwana a gidanmu ba, ni ce kawai Mamina bata barina na kwana a gidan su Umaima saboda wai gidanmu ya mata girma ita kaɗai, ta fi son tana jin mostina. Mami ta sani na ɗebo mana namu abincin, muka ci muna kallo hankali kwance, hira muka ɗan taɓa da Mami sannan nake faɗa mata ma yanda muka yi da Malam Abbo akan maganan musabaƙa da hukuncin makaranta, da mamaki dai na kalli Umaima hankalinta kwance bata tashi hankali ba, Mami ce dai ta nuna ɗan damuwanta sannan ta mana faɗa sosai akan mu dage mu mayar da hankali, ta kuma ƙara mana da nafilfilu da kuma addu'oe da za muyi saboda exam's da za mu fara gobe da yardan Allah, ba mu wani jima ba na tashi na shige ɗaki bayan na yiwa Mamina sai da safe, ina shigewa Mami ta dubi Umaima ta ce, "yarinyar Mami kada ki sanar da ita gaskiyan abinda ake ciki, ki ƙyaleta dai ku dage ku mayar da hankali, kinga yanzu ta saki ranta, nasan idan ba ta haka aka ɓullo aka mata wayo ba, to Banafsha ta dinga cin rai kenan." Murmushi Umaima tayi ta ce, "Insha Allah! Mami ba zan sanar mata ba, zan dai nuna mata nima na damu mu ƙara mayar da hankali." "Yauwa ƴar kirki, Allah muku albarka duka ya ba ku sa'a ku ciyo na ɗaya a musabaƙa, flying color result a boko" cewan Mami tana murmushi. Umaima amsawa ta yi da, "Ameen" sannan ta yiwa Mami sai da safe ta shige ɗakin Banafsha, Mami ma hamdala tayi sannan ta kashe kayan kallon ta koma nata ɗakin, sai da ta gabatar da shafa'i da wuturi da wasu nafilfilun sannan ta kwanta. Na fito wanka ina ƙoƙarin shumfiɗa darduma Umaima ta shigo, kallon yanayin fiskanta ya sa na tambayeta ki lafiya, cikin damuwa Umaima ta ce, "Masoyiya maganan musabaƙan nan ne ya dame ni." Kwantar mata da hankali nayi, na ce mu dage da addu'a da kuma karatu, sannan in Allah ya yarda ni ma daga yau ba zan sake irin wannan dena zuwa makarantar ba, da ƙyar na shawo kan Umaima ta shige wanka, tana fitowa ta saka kayana muka yi nafilfilunmu da addu'oe sosai, sannan muka kwanta, da asuba kuwa muka tashi muka hau karatu saboda exam's. Ya Danish taƙaici da ya cika sa ya masa dama-dama, ko gidan bai koma ba daga nan ya yiwa motansa key ya wuce wajan aikinsa da ke Camaroon, idan ya koma Sunday da yamma sai Friday da yamma yake zuwa, weekend kawai yake zuwa yi a mubi. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Habiba muhammad Yusuf Ɓingel kabi My Heartbeat Masoyiya bealky اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 31 _ 35 Washe-gari Abbaa da kansa ya saka Nana ta kawo wa Umaima uniform nata gidanmu, Umma sai cin rai take yi tana ta fushi akan Umaima ta kwana a gidanmu, amma Abbaa ko a jikinsa, Umma haushi kaman ya kasheta ga shi Ya Danish ba ya gida, kuma babban yaya ba ruwansa, ya mus'ab da ke Camaroon ma ko yana nan ba ruwansa, Ya Danish ne daman mai biye mata. Mun yi wanka mun shirya tsaff muka fito, abin karyawanmu da komai muka samu Mami ta jera mana a kan centre carpet na palourn, zama muka yi muka cika cikinmu yanda ya kamata, sannan muka yiwa Mami sallama ta ba mu kuɗin mashine da na kashewa muka fice, cikin sa'a muka samu mashine kuwa da wuri, ya ajiye mu a makaranta muka shige hall na exam. Haka rayuwa ta dinga tafiya da daɗi da babu daɗi dai sai haƙuri, mastalolin rayuwa da ƙalubalen rayuwa gare ni kullum ƙara gaba suke yi, saboda daga halayyan Mamina babu wanda ya canja kullum gaba-gaba abun yake yi, ni a tunanina abinda wancan stohon ya mini zai sanya Mamina gyara kura-kuranta, amma ina Mamina ci-gaba tayi da harkokinta, sam-sam Mamina bata jin ƙira dan ta riga da tayi nisa, kullum dai magana guda ne, idan na ce ta dena wannan rayuwa, sai ta mammakeni kuma ta ce sana'a ce dan ta rufa mana asiri,nidai wannan sana'a banga alfanunta ba, sai dai ban da yacce zan yi idan ba addu'a ba. Maganan makaranta kuwa na dage sosai na mayar da hankali muna exam's namu hankali kwance, sannan a tahfiz ma ina ƙoƙari yanda ya kamata, tsakanina da Malam Abbo kuwa yanzu ya zama kaman yayana dan yana yawan mini faɗa da nasiha, sannan wani irin shaƙuwa na neman shigowa tsakaninmu wanda ni dai ban farga da hakan ba sai da shaƙuwan tayi nisa. Sati biyu muka kwashe muna exam's, sai ranan Alhamis muka kammala, daga ranan kuma muka yi wa makaranta bye-bye, saboda musabaƙan namu week da za'a shiga ne. Kaman ko wanne weekend, yau ma da yake Saturday da wuri muka je tahfiz muka dawo, tun daga compound na gidanmu da na shigo na ga wata dalleliyar haɗɗaɗɗiyar Mota, lumshe ido nayi kawai ina ambaton sunan Allah dan nasan ba zai wuce wani baƙon Mamina tayi ba, taɓe baki nayi ina faɗin ko wani jarababben ne da sanyin safiya haka oho, sai da na seta zuciyata na shanye taƙaicin da zan tarar a ciki tun ban shiga ba, sannan na tura ƙofan palourn na shiga da sallama, daga muryan wanda ya amsa mini sallaman na sheda baƙon da Mami ta yi da sassafen. Ƙarisa shiga palourn nayi kai na a sunkuye, durƙusawa nayi har ƙasa na ce, "Sannu da zuwa Alhaji." Alhaji Mukhtar na washe baki ya ce, "Sannu ƴar albarka, sannunku da dawowa ko." Amsawa na yi har yanzu ban ɗago ba balle mu haɗa ido, a haka na gaishe sa ya amsa, ya ce na je na huta na karya zuwa anjuma zai ji karatun nawa, ba musu na amsa na miƙe na shige ɗakina, ina shiga na faɗa kan gado tare da ɗaga hannayena sama na ce, "Ya Rabbi ga bayinka nan, ka fi ni sanin abinda suke ciki, ya Rabbi ka shirya su ka gyara rayuwansu, ya Rabbi kada ka kama zuri'arsu da laifin da basu ji ba, ba su gani ba, don kuwa ƙur'ani mai girma ya ce "az- zina dailun (zina bashi ce)", Allah ka shiryamu duka, ka shiga stakaninmu da biyan bashin da ba mu ci ba", ina ƙarishe addu'ana na miƙe na cire uniform nawa, ina ƙoƙarin fita sai Mamina ta shigo, murmushi ta sakar mini ta ce, "Sayyada Faɗimah a zo a karya, kada ulcer ta kama mini 'yar fari, 'yar auta." Murmushin nima na yiwa Mamina ban ce komai ba, na bi bayanta muka fice, abin karyawa na samu ta zubo mana ni da ita, zama nayi amma na kasa cin abincin, kasancewan Alhaji Mukhtar na palourn duk da dai hankalinsa na kan wayansa ne, Mamina ganin naƙi ci sai ta gusturo sinasir ɗin ta kai mini baki, ni kuma na buɗe bakina a hankali ina karɓa, a haka ta dinga bani a baki har na ƙoshi, sannan ta cigaba da cin nata, Alhaji Mukhtar da ke kallonmu sai yayi murmushi ya ce, "Lallai Ramlah kin shagwaɓa mini yarinya da yawa, budurwa da ita kina mai da ta 'yar goye, yarinyar kirki kar ki biyewa Maminki fa, ke babba ce yanzu." Ƙasa nayi da kai na ina murmushi, Mamina kuwa kallon soyaya ta yiwa Alhajin nata ta ce, "wannan jaririyar ce babba? Banafsha ta wuce na sa zani n goya ta ne Alhaji? Ita ce fa 'yar fari kuma 'yar autan Maminta." Alhaji Mukhtar ma yana murmushin ya ce, "Amma dai wasa kike yi, Banafsha kar ki yarda fa ta ce miki auta, ƙannenki na zuwa." Mamina ta ce, "bayan ita ba kowa, daga ita ba ƙari, tal ɗin Maminta, shalele gudan stokar miya." Alhaji idanuwansa akan wayansa ya ce, "yarinya ɗaya bata ishe mu ba, dole ki haifo mini wasu." Kai na a ƙasa ina sauraran maganan su Mamina, jin abinda Alhaji ya ce sai nayi saurin ɗagowa dan na kalli yanayin Mamina, a tunanina zan ga tayi murmushi dan ita ma tana son haifa mini ƙanne, amma sai saɓanin hakan na gani, Mamina ta haɗe fiskanta ta yi kicin-kicin da shi, Alhaji Mukhtar kuwa hankalinsa kwance yana lasta wayarsa sai ma murmushin da yake yi, dan yasan ya stokano masoyiyarsa Mami kuma shi daman burinsa kenan, saboda wani shiri da yake yi na daban. Mamina ganin ma yana murmushinsa ya manna mata hauka, sai ta miƙe ta wuce ɗakinta, ni kuma na tattare kwanukan na mayar kitchen, har da wanda Alhaji ya ci abinci a ciki, na Juyo zan shige ɗaki sai Alhaji ya dakatar da ni ya ce na zo, dawowa nayi na samu waje a nesa da shi na zauna a ƙasa, yana murmushi ya ce, "Yarinyata Banafsha ya karatun? Fatan kun gama exam's lafiya?" Kai na a ƙasa na ce, "Lafiya Alhamdulillahi, Alhaji." "To Masha Allah! Allah sa result tayi kyau, Ya karatun musabaƙan kuma? Yaushe za ku yi?" Kai na a ƙasa har yanzu na basa amsa da ranan da za mu yi, jinjina kai yayi ya ce, "To shikkenan, zuwa dare Insha Allah za mu duba karatun, yanzu je ki huta, zuwa anjima za mu je anguwa Insha Allah." Miƙewa nayi na masa a huta gajiya na shige ɗaki na, shi ma miƙewa yayi ya shige ɗaya ɗakin, ruwa ya wasta ya kwanta tare da jawo wayansa yayi dialing wani number da sunan "My Son" ya ke ɓaro-ɓato, ba jimawa aka ɗauka, Alhaji Mukhtar yana murmushi ya ce, "Chief of the air staff." Wani haɗaɗɗen murya ne ya murmusa yanda sai da sound na murmushin ya fito, sannan cikin yanga ya ce, " morning Sir." Alhaji Mukhtar murmushi yayi tare da girgiza kai ya ce, "BUNAYD Allah ya shiryeka." A hankali kaman mai raɗa ya ce, "Ameen Papi." "Ya General?" "General yana gidansa Sir." Girgiza kai Alhaji ya kuma yi ya ce, "zan saɓa maka Bunayd, ina ubanka kana ce mini wani Sir." Murmushi ya kuma yi ya ce, "sorry Sir!" Alhaji ya ce, "Ubanka General ne Sir, yaushe za ka shigo Kano?" "Soon zan shigo, kasan za'a yi bikin Abeed in next 3 months." Alhaji ya ce, "Masha Allah! Ya fi masa ai yayi aurensa, kada ya biyewa duniya wai sai yayi iyayi, yanzu mutuwa araha take, kar mutum yaga kullum yana sama kaman stunstu ya ɗauka shi ba mutuwan zai yi ba, to azara'ilu ko a duniyar wata kake lokacinka na cika zai zare ranka, balle jirgi da nawa aka yi, idan akwai mai ƙararren kwana a ciki ai hastari jirgi ke yi, to gwanda tun wuri kasan abinda ka adana kamun ka wuce babu masu maka addu'a." Bunayd a ɗaya ɓangaren murmushi yayi bai ce komai ba dan yasan da shi Papi ke yi, Alhaji ya kuma cewa, "ko ka fito da mata ko kuma daga kai har ubanka General ku ji anbada ka sadaka, sadaka yalla zan ba da kai a masallaci, in ana ƙiran macen sadaka ta Annabi, to kai za ka zama na Annabi, bari lokacin da na ɗiba maka su cika." "Byee Sir, my regards to Adamawa" yana gama faɗa kitt ya daste ƙiran. Alhaji murmushi yayi tare da cewa, "Allah ya muku albarka" yana gama faɗa ya gyara kwanciyansa ba jimawa bacci tayi gaba da shi. Ɓangaren Mami ma tana barin palourn ta bi lafiyar gado ta koma baccinta, cike da taƙaicin Alhaji Mukhtar, maganansa ya wuce stakaninsu ga shi har a gaban yarinyarta yana faɗa mata maganan aure, ita kuma ga shi duk abinda zai mata ta kasa rabuwa da shi, a rayuwanta gaba-ɗaya wannan ne karo na biyu da taji tana matuƙar son wani har tana jin ba za ta iya rabuwa da shi ha, Alhaji Mukhtar na cin albarkacin wannan soyayyan idan ba haka ba, da tuni ba wannan maganan ake yi ba. Ɓangarena ma baccin ne yayi gaba da ni, sai wajan azahar na tashi, fitowa nayi naji gidan shiru alaman duk basu tashi baccin ba, sai na shige kitchen na kunna gass na hau haɗa mana abincin rana, fried rice da yaji ice fish da haɗin coslow na mana, sai da na gama sannan na koma ɗakina lokacin ana ƙoƙarin shiga sallah, wanka nayi na ɗaura alwala na gabatar da sallah na sannan na fito dan tashin Mamina, amma sai na same ta zaune a palourn ta sha kyau, ina isa wajanta da murmushi sai kuma ga Alhaji ya shigo, alama daga masallaci yake, ƙasa nayi da kai na, Mamina ta ce, "je ki kawo mana abincin mu ci, mu yi la'asar za mu fita duka da Alhaji." Miƙewa nayi na haɗo mana abincin, na Alhaji na ajiye masa, na ajiyewa Mamina nata, sannan na juya, nawa na ɗebo na shige ɗaki, ina ci ina game a wayan Mamina da na ɗauko, binciken da na saba yi ko zan ci karo da layin wani ɗan uwan Mamina a wayanta na yi, amma ba ko alaman abinda ya shafi layin wani nata, ganin haka sai na dinga game kawai ina cin abinci, har aka ƙira la'asar, sannan nayi sallah na kuma wanka na sanya riga da skirt na swiss-less, ba ƙaramin kyau kayan ya mini ba, kuma ya zauna a jikina ɗamas, mayafina na yafa na fito, lokacin Alhaji da Mamina ma sun shirya, Mami kallo ɗaya ta mini ta ce na koma na sako hijabi, cunna baki nayi ina shagwaɓe fiska na ce tayi haƙuri, amma ta dage sai na sako hijabi, Alhaji ne ya bata haƙuri tunda a mota ne ta kyale ni da mayafin tunda ba ƙarami bane, Mamina da ƙyar ta ƙyale ni tana wasta mini mugun kallo, wanda nasan nufinsa bai wuce ta ce nasan halittan da Allah ya mini ko ina a cike amma bana son hijabi, ni abun har ɗaure mini kai yake yi, Mamina kaman wacce ta fito a jikin bishiya ba iyayene suka haifeta ba, ko kaɗan bata damu da kanta ba, burinta a rayuwanta komai nine, bata damu da mutuncinta ba tana kule-kulen maza, amma ni ko saurayi har yau bani da kuma ta hanani waya ma, ajiyan zuciya kawai na sauƙe tunda ta bar ni naje hakan ba komai, Allah dai shi ne mai starewa. Tare muka fito duka, Alhaji ya shiga mazaunin driver, Mami ta zauna a gefensa kujeran mai zaman banza, ni kuma na buɗe gate, sai da motan ta fita sannan na kulle gidan gaba-ɗaya na nufi motan, a ƙofan gidan su Umaima na hango ya Danish da yake shigewa gidan bai ma kalleni ba shi, murmushi na sake na abinda na rashin mutuncin da na shirya masa, gidan baya na shige Alhaji ya ja mota muka shige gari, Japsal Shopping-mall muka fara zuwa, waje ne na sayayya kuma kayaki ne masu kyau da kuɗi a can, sayayya Alhaji ya mana ba kaɗan ba, kama daga dangin kayan sawa, kayan kwalliya, kayan abinci, kayan abun sha da su snacks, muna gamawa da sayayya kuma ya wuce da mu ADU, nan ma sai da ya mana ordern abinda za mu ci, kowa aka kawo masa abinda yake so, muka cika ciki, muka yi takeaway, ƙara zaga gari yayi da mu, yawo muka yi sosai kaman ba gobe, idan ka ganmu za ka ɗauka Mami da Alhaji, mata da miji ne da kuma ni ƴar su. Sai da yamma tayi liss muka dawo da kaya niƙi-niƙi, Alhaji ya kashe kuɗi ba kaɗan ba, kuma ya ce kada Mami ta yi girkin dare, wannan takeaway ya ishe mu, idan da wani abin ma zai fita ya nemo, ni kuwa daman na jidowa Umaimata nata tunda nasan mayyar ice cream ce ita da naman kaza, muna iso wa, na sauƙa na buɗe ƙofa Alhaji ya shige da motansa, kayan da na jidowa Umaima na ɗauka na ce, "Mamina bari na bawa Umaima nata", kamun Mami tayi magana tuni na fice a gidan da sauri saboda kada ta dakatar da ni, ai kuwa hakan aka yi, ƙwala mini ƙira ta dinga yi amma na gudu, Alhaji murmushi yayi tare da riƙo hannun Mami ya ce, "Amarya ta mu shiga ciki ko." Wani kallo Mami ta masa tare da ƙwace hannunta ta shige fuuuu! Ga haushin Alhaji ga haushin Banafsha ta fita ba hijabi. Ni kuwa ina shiga gidan su Umaima na dinga leƙe-leƙen Ya Danish, amma ban gansa ba, kuma dai motansa na gida, nasan ba zai wuce yana part nasu ba, shigewa cikin gidan nayi ba kowa a palourn, sallama nayi na nufi ɗakin su Umaima, samunta nayi tana guga, murmushi na sakar mata, ta ce, "Masoyiya irin wannan kyau haka, komai Masha Allah! Daga ina?" Ledan hannuna na miƙa mata na ce, "Ga tsaraba tawan." Umaima kaman za ta fire ta ce, "Wayyo! Allah bar mini ke Banafsha, Mamina Allah ƙara buɗi, wayyo naman kaza da ice cream, kutt har da shawarma, oyoyo chocolate" faɗin Umaima tana dariya. Zama nayi a gefen gadonta na ce, "Mun godewa Allah da ba'a ƙauye kike ba, ko gidan talakawa da abin ya fi haka, Abbaa yana da kuɗinsa, yayyunki ma haka, kuma Umma na business, Ummu ma ba'a bar ta a baya ba, kuma babu wanda ba ya saya miki, amma idan kika ga kaza da ice cream kaman me, gaskiya idan Allah ya kai mu Abuja za ki ba da mu, muna zuwa saudi kuwa nasan sai na dinga riƙe ki, saboda kada a samu masu jan ki da dajaja(kaza da larabci), kinsan larabawan Makkah wasu yan albarka ne, wasunsu iskanci suke da mutane." Hararana Umaima tayi ta ce, "To zabiya, kanki ake ji, ki bari idan munje makkan sai mu tabbatar, ba kyau shedan zurrr." Nima rama hararan nayi ma miƙe na ce, "sai anjuma bari na shirya ki same ni a ƙofa mu wuce tahfiz." Amsawa Umaima tayi, na fice na shige ɗakin Ummu na gaisheta, sannan na fito ina ta kan leƙe-leƙe ban hango sa ba, yaya babba ne ya shigo gidan, da murmushi na ɗan rusuna na ce, "Sai babban yaya! Allah taimaki babban yaya." Dariya yaya babba yayi, ya ce, "sistor ba'a raba ki da abin dariya, kun gama exam's lafiya?" "Alhamdulillahi babban yaya, ya Auntynmu." "Tana lafiya, tunda kun ƙi zuwa gidan mu, ga baki ga hanci amma bakwa son shiga, daga ke har Umaima, bealkysou ce kawai ke shiga." Murmushi nayi na ɗan sosa kai, dariya yayi ya ce, "Allah shiryaki sistor, wannan kyau haka daga ina zuwa ina?" Na buɗe baki zan basa amsa cikin kunya, sai muka jiyo muryan Umma tana masifa wai ta ƙirasa ya tsaya magana da fistararriyar yarinyar nan ƴar karuwa, yaya babba haƙuri ya bani da ido kawai ya wuce, ni kuwa fakan idon sa nayi ganin ya juya na aikawa Umma da murguɗa baki, juyawa nayi ina tafiya na, kaman daga sama kawai naji an zuba mini ranƙwashi aka ce, "Dan uwarki, fistararriya uwar tawa kike wa gastine da baki?" Ina ɗagowa, idanuwana suka sauƙa akan Ya Danish, cikin zafin ranƙwashin na ɗaga hannu zan maresa, amma sai ya riƙe hannun nawa ƙam na kasa mosta sa balle ƙwace sa, wani kallo ya wasta mini ya ce, "mara tarbiyya kawai, dube ki haka kike yawo, uban wa za ki ja hankalinsa da wannan ƙazamin jikin naki, mai rijiyan kasuwa kowa zura gugansa yake, mara aji kawai." Taƙaici ne ya rufe ni na maganganun sa, na ma rasa da me zan rama ga shi har yanzu ya ƙi sake mini hannuna, idanuwana ne ke ƙoƙarin kawo ƙwalla, amma ƙoƙari nake wajan maida su, cikin dakewar zuciya na ce, "sake mini hannuna ni ba sa'ar yinka ba ce, wanda bai san darajar uwar wani ba balle a kai ga tasa" ina faɗa na ƙwace da ƙarfi, sai da na staya na ƙare masa kallo sama da ƙasa sannan naja staki na ce, "Ni ko iskancin nake yi ai kasan na wuce wa irinka, na wuce yinka, na fi ƙarfinka, ba ka da abinda za ka isar da ni, ka yi kaɗan abinka yayi kaɗan, ka je a sake maka kaciya tukunna, riƙe hannuna ba zai sa naji komai a kanka ba, saboda kallon jariri nake maka, abinka kuɓewa ma ta fi sa a waje na, mtsww!" Ina gama faɗan haka na juya da sauri-sauri na bar sa a wajan tsaye da buhun mamaki, ni ko ina ficewa na juya na harari gidan, sannan na murmusa dan nasan ko banza na faɗa masa magana, ina dariya kaman ba ƙalau ba na shige gidanmu. Ya Danish mutuwan tsaye yayi, jin abinda yarinya ƙarama ke faɗa masa, haushinta da stananta suka ƙara cika sa, ƙwafa yayi ya ce, "ko na fi karfin zura gugana a rijiyar mutane da yawa, to tabbas sai na gwada miki karatuna ya fi ƙarfin na 'yan iskan abokan iskancinki" yana gama faɗa shi kaɗansa ya shige sashinsu ya fasa shiga cikin gidan ma, saboda taƙaicin Banafsha. Ni kuwa ina shiga tun ba'a faɗa mini ba na buɗe motan Alhaji na dinga jidan kayan ina kai wa ciki, sai da na gama sannan na kalli Mamina a sace na wuce ɗakina, shiryawa nayi na fito na ce, "Mami sai na dawo." "A dawo lafiya" Mamina ta faɗa a taƙaice, na fice a gidan, a ƙofa muka haɗu da Umaima muka wuce tahfiz, sai da aka tashe mu sannan muka kamo hanya muna hira, na faɗa wa Umaima yau Malam Abbo bai zo ba Allah ya sa lafiya, amsawa tayi da Ameen tana kallona tana murmushi, saboda Umaima ta gama fahimtan akwai abu a zuciyan Malam Abbo game da Banafsha. Tun daga hanya muka raba tasha ta yi gidansu, nayi namu dan kar Ya Danish ya ganta, ina isa gida na yi sallah na je kitchen na ɗauko rabona na ci, sai da muka yi isha'i, sannan muka zauna dukanmu, Alhaji yana ja mini aya ina ƙarisawa, haka muka dinga yi har dai muka yi iya dai-dai izu arba'in ɗin da za muyi musabaƙan a kai, ko ina ya canko ina idawa dai-dai, kuma yana tambaya ina basa amsa dai-dai, gyara biyu kawai ya mini, sai da muka yi sosai sannan ya kulle ƙur'anin ya sa na mayar da shi, muka zauna muna kallo, ba jimawa na musu sai da safe, sai da nayi karatu sosai na yi nafila da shafa'i da wuturi, sannan nabi lafiyan gadona na kwanta bayan nayi addu'an bacci. Mami da Alhaji ba laifi yau ba'a yi faɗa ba, amma ko da suka shiga ɗaki Alhaji nafilfilu kawai ya dinga yi har Mami tayi bacci, shi kuma ya tattara ya koma ɗaya ɗakinss ya kwanta, bayan yayi waya da matarsa Hajiya Sa'adatu. Washe-gari haka muka je tahfiz muka dawo, nan ma dai Malam Abbo bai zo ba, ya Danish dai ya gama haɗa irin muguntan da zai mini, sai dai cikin rashin sa'a kuwa ba mu haɗu ba har ya koma da yamma, haushi kaman ya kashe sa, amma ya gama cin alwashin wata satin zai gyara mini zama, Alhaji Mukhtar kuwa sai washe-gari Monday sannan ya sallami Mamina, ni kuma ya mini faɗa sosai akan na dage, idan nayi ƙoƙari shi ma zai mini kyauta duk abinda nake so, sannan ya ƙara ƙarfafa mini guiwa sosai, sai ya kama hanyan Yola, yana isa ya wuce airport jirginsa ta ɗaga sai garin kano kanawan dabo. Ranan Monday munje tahfiz amma boko kam mun ƙyale sa sai result ta fito kuma next semester, a ranan aka gama komai da komai a tahfiz na shirin musabaƙa saboda daga ranan Laraba za'a fara kuma har sai asabar a gama saboda makarantu da yawa ne za su yi musabaƙan, an tashe mu akan ranan talata kada muje kowa ya huta kuma yayi karatu yayi addu'a, ni da Umaima kuwa washe-gari talata maimakon karatu sai muka shirya abinmu muka tafi gidan yaya babba duk da kusa-kusa ne amma yini muka kai masa tunda ya ce bama zuwa, kuma zai yi fushi, munje gwanin daɗi-daɗi Amaryan sa mai ɗan matashin juna biyunta ta amshe mu da fara'a, amma tunda yaya babba ya dawo taga yanda muke wasa da dariya da shi, musamman ni sai ta fara haɗe fiska tana hararata, kamun ka ce me ta tsawwalawa kanta wai kishi take da ni, amma daga ni har Umaima har yaya babba babu wanda ya hararo jirginta, abinda ya dame mu muke yi. Sai da yamma tayi liss, sannan muka ma Amarya Hindatu sallama, amma sai wani cin magani take yi, ba mu damu ba yaya babba ya sako mu gaba muna tafiya muna hira har gida, kallona yayi yana murmushi ya ce, "su sistor an kusa zama graduate, ga kuma za'a ciyo mana kyauta a musabaƙa, sannan kuma za'a amarce." Ina dariya na ce, "wa ya faɗa maka haka babban yaya? Amarci kuma?" Ya kabeer (babban yaya), yana dariya ya ce, "Faruq ne ya faɗa mini ai, wai haka kika faɗa musu, kuna zama graduate sai aure, inyee! Waye wannan mai sa'an? Ni na ɗauka ma da Danish za'a yi, irin wannan stamar tsakanin naku ai ta love ce, gaskiya koma waye a basa haƙuri muyi tuwo na mai na." Haɗe fiska naayi, girar sama da ƙasa duk na haɗe su, na tura baki tare da bankawa Umaima harara kaman ita tayi maganan na ce, "Ni na tafi gidanmu sai gobe." Yaya babba yana ta ƙira na amma naƙi juyowa, dan sosai ya ɓata mini rai, ni ba aure ne a gabana ba, ba zan je a dinga wulaƙantani ba, kuma ko auren zan yi har abada babu abinda zan yi da Ya Danish, ni ban taɓa jin na tsani mutum a duniya yanda na tsani ya Danish ba, a haka rai a haɗe na shige gida, Mami ta kalle ni kawai ta girgiza kai, cikin sigan rarràshi ta ce, "Wa ya taɓa fitilar Maminta? Shalelena, Sayyada Faɗimah, autar mata, shugabar mata, gudalliyan Maminta." Tura baki nayi, kaman zan yi kuka na ce, "Mami ba kina ganin babban yaya ba, wai ai...wai... wai ai..uhmñ!" Mami murmushi tayi ta ce, "kina ta cewa wai wai kin kasa faɗan abinda ya faɗan, wai me?" Langwaɓar da kai nayi na tura baki na ce, "uhmñ! Ni dai ba ruwana kada ma yan Ameen su amsa magana ya wuce." Mami taɓe baki tayi ta ce, "Idan tayi tsami zan ji, in kuma sun riga sun amsa, shikkenan ko mutuwa za kiyi yess ne, indai alkairi ne." Tashuwa nayi kawai na wuce ɗakina, jin Mamina za ta ƙara nata akan na babban yaya. Babban yaya kuwa dariya ya dinga yi, Umaima tana taya shi ta ce, "yaya ka kora mini Masoyiya kuma kasan ba wannan maganan tsakaninta da ya Danish, ranan ina laɓe ina ganin su har da ranƙwashinta yayi, ranan da ka zo da yamma." Murmushi yaya babba yayi ya ce, "Nima na gani ai, na sani Umaima, da gangan na faɗa, amma na sani Danish da Banafsha ba wannan magana, mutane kaman masu ganin hanjin junansu,ya riga ma da ya ɓata rawansa da stalle babu ta yanda za'a yi ta ƙaunace sa." Umaima dai murmushi tayi ta shige gida yaya babba kuma ya juya ya koma gidansa, yana shigowa ya kalli matarsa ta haɗe nata giran sama da na ƙasa, fiska kaman an haɗo mummunan hadari, cikin mamaki ya dubeta ya ce, "my love me ya faru? Ko baby ne ya naushe ki? Ya faɗa yana murmushi tare da zama a gefenta. Stam! Hindatu ta miƙe ta koma gefe ta zauna, tare da juyar da kai, yaya babba bai kawo komai a ransa ba akan su Banafsha, kawai ya ɗau abun akan ko fushin masu ciki ne, haka ya dinga lallaɓata, da ƙyar ta haƙura sannan ta ce ya shiga tsakanin Banafsha da zuwa gidanta bata so, babban yaya kam mamaki ne ya kashe sa a zaune, wato daman abinda ya sanya ta sauya fiska tun ɗaxu kenan, girgiza kai kawai yayi ya lallaɓata komai ya wuce. Banafsha duk da tasan gobe ba lallai a fara da su ba, amma ta dage da karatu da addu'a, duk da gefe guda na zuciyarta tunanin rashin zuwan Malam Abbo kwana biyu ne cike fam a ciki, haka kawai take kewansa sam bata jin daɗin rashin ganinsa. Ɓangaren Umaima ma karatun da addu'an tayi sosai, Nana ce ta shigo ta ce, "yaya Umaima wai inji Umma ki zo." Miƙewa tayi ta fice, ɗakin Umma ta shiga da sallama, bayan ta zauna a gefe ta ce, "Umma gani nan." Rai a ɓace Umma ta dubi Umaima ta ce, "Umaima! Umaima! Umaima! Sau nawa na ƙira sunanki?" Umaima ta ce, "sau uku Umma." "Umaima kinsan dai ni ce uwarki ko? Ni na stugunna na haifeki ba wata banza ba ce ta haifa mini ke, kibar ganin ansaka miki sunanta tana nuna tana sonki, to duk soyayyan munafurci ce ba ta gaskiya ba, Umaima ki nistu ki shiga hankalinki da ni, kada ki bari rai na ya ɓaci kiga fushina, ko kuwa na miki baki akan wasu mutane daban, Umaima uban wa ya ce kije gidan kabeeru da wancan fitsaratun yarinyar?" Umaima tura baki tayi ta ce, "Umma kiyi haƙuri, wallahi ni ba ruwana babban yaya ne ya ce muje da ita." Umma hararan Umaima tayi ta ce, "Dan ubanki rufe mini baki, munafuka kawai, ƙarya za ki mini? Bansan halinki ba ne ko me? Sau nawa ina faɗin ki fita harkan yarinyar nan bana so, bana so amma kin mini kunnen uwar shegu kinƙi ji, to kada ki bari rai na ya ɓaci." Tura baki Umaima tayi ta ce, "ki yi haƙuri Umma." "Tashi ki bani waje kamun na karya ki yanzun nan, mara zuciya kawai wacce bata gaji uwatta ba." Faɗin Umma kaman za ta kifawa yarinyar tata mari. A ɗari Umaima ta tashi ta fice, ta koma ɗakinsu tana faɗin, "Allah huci zuciyanki Umma, Allah shirya mana ku iyayenmu." Washegari Umaima da Banafsha suka shirya staff suka tafi tahfiz, Banafsha da Malam Abbo ta fara yin tozali, farinciki kaman ya kasheta, har Malam Abbo sai da ya kusa fahimtan hakan saboda ya ga wani irin murmushi da take sakar masa, abubuwan da ya kamata suka yi sannan aka ɗauki ɗalibai aka tafi wajan gabatar da musabaƙa, makarantu ne kusan nawa, haka aka fara gabatar da musabaƙa, ɗalibai kowa na iya ƙoƙarinsa, amma har aka tashi na yau ba'a taɓo ɗaliban makarantan su Banafsha ba, sai da suka dawo sannan Banafsha ta sa Malam Abbo a gaba da shwagaɓa wai me ya sa kwana biyu bai zo ba, Malam Abbo murmushi kawai ya mata ya ce su tafi gida ta ci-gaba da dagewa da karatu. washe-gari ma haka aka yi musabaƙa lafiya-lafiya kuma dai ba'a iso su Banafsha ba, Laraba, Alhamis, juma'a duka ba'a iso su Banafsha ba, kuma abu na ta kan tafiya, ɗalibai masu ƙoƙari suna yi, wasu kuwa ana musu gyara, wasu kam ma dismiss nasu ake yi saboda they're not fit and compited, ɗalibai da dama wasu akwai ilimin, akwai kuma ƙoƙarin, amma ba su da confidence na tsayuwa a gaban dubban jama'a su gabatar da abu, wanda kuma wannan confidence ɗin shi ake buƙata a wajan ɗalibi, wani sa'in ma shi aka fi buƙata fiye da ƙoƙarinsa ko iliminsa, so dan haka yaranmu students ku dage, ku sa a ranku kuna da ƙwarin guiwan stayuwa a gaban duniya kuyi magana, just feel you can stand and talk for whole world, wannan courage shi ake buƙata, Allah ya taimaka wa yaranmu masu karatu da mu kanmu, Allah buɗa basira ya dafa mana a ko wanni hali da juyin rayuwa. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKI NE Hafsat Umar اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 36 _ 40 ⭐ KANO STATE A babban filin sauƙan jirgi na garin Kano, jirgin su Alhaji Mukhtar yayi landing, yana sauƙa ya samu already driver na jiransa, yana isowa wajan motan sai driver ya buɗe masa gidan baya ya shiga, sannan ya kulle ya koma ya shige ya ja motan suka nufi Railway estate, anguwan manyan ƙwari kenan a Kano, daga sunan kunsan ba wajan cin miyan lami bane. A gaban wani katafaren, shirgegen, haɗaɗɗen gida wacce ke ɗauke da wata arniyar gate ga sojoji ko ta ina, driver na horn aka buɗe musu suka danna hancin motan cikin gidan, subhanallahi! Wata munafukar estate ce, upstairs guda biyu, sai haɗaɗɗun plat guda biyu su ma, ga motoci sun kai goma manya-manya masu shegun kuɗi, upstairs na farko Alhaji Mukhtar ya nufa fiskansa ɗauke da murmushi, yana tura ƙofan ya shiga da sallama, da wata kyakkyawar matashiyar budurwa wacce ba za ta wuce sa'ar Banafsha ba ya fara karo, murmushi ya sakar mata tana masa oyoyo, hugging nata yayi ya ce, "Maman babanta sannu ko." Murmushi budurwan ta saki ta ce, "Papi staraban Adamawa." Alhaji shafa kan 'yar budurwan yayi ya ce, "Majeeder tun ban huta ba?" Murmushi kawai tayi, Alhaji ya riƙo hannunta suka ƙarisa shigewa palourn, har suka haura sama da yake part na Alhaji, suna haurawa kuwa sai ga wata hamshaƙiyar mata kyakkyawa, wacce kana ganinta kasan ita ce mahaifiyar Majeeder, Hajiya Sa'adatu kenan uwargida ga Alhaji Mukhtar, harara Hajiya ta bi Majeeder da shi ta ce, "Jeedderh ban aike ki ba ne, me kika tsaya yi?" Majeeder tura baki tayi ta juya, Alhaji Mukhtar murmushi kawai yayi bai ce komai ba, shi ne ya ce, "Hajiya Barka da gida." A gadarance Hajiya ta ce, "Sannu da dawowa Alhaji." Amsawa yayi kawai ya shigeta ya wuce ɗakinsa, sai da ya rage kayan jikinsa ya zauna bakin gado tare da sakin murmushi ya ce, "Allah Sarki duniya, ba dole mu bi mata ba, ai dole maza su nemi matan banza, mace ce a gidan sunna wai bata san yanda za ta kula da mijinta ba, sai ka je wani wajan sai a dinga tarairayarka, ga shi dai saɓon Allah ne a wajen, Astagfirullah! Allah na tuba, Allah ka mallaka mini Ramlah idan ita alkairi ce a gare ni, ba dan halina ba ya Rabbi." Yana gama magana ya miƙe ya shige toilet ya wasta ruwa sannan ya zo yayi sallolinsa ya jawo system nasa ya fara duba ayyukansa, yana gamawa ya bi lafiyan gado ya kwanta, yana son ya huta saboda nan da kwana biyu zai tafi Russia akan business nasa da wani abun gaggawa ya taso. Hajiya Sa'adatu tana ganin Alhaji ya shiga ɗakinsa ta juya ta koma nata, tare da fidda waya tana ta magana akan nata business ɗin ita ma. Mata mu gyara, abun haushi da iya matan masu kuɗi ke kasa kula da mazajensu, saboda boko ta jiƙa su ko issuen harkokinsu to da sauƙi, amma baiwar Allah kina salamatu 'yar malam muhammadu ke ba juya dubu ba balle ya koma dollar, aikin me kike da za ki kasa kula da miji ki tarairayesa? Maza dai ƴan haƙuri ne, balle ma a wannan zamani da muke ciki suke ganin mun fi su yawa, to ki kula ƴar uwa, aure ya fi gaban wasa, idan mijinki ya bi matan banza ke kika nema, idan mijinki ya miki kishiya babu niya wannan ma ke kika jajuɓo ma kanki, Aradu mata iyayenmu da mu kanmu da kuma ƙannenmu kowa ya gyara halinsa. Majeeder tana tura baki ta shige ɗakinta da ke nan a ƙasa ta sanya after dress ta fito, mota guda ta ɗauka da kanta ba driver tayi driving ta je ta amsawo Hajiya saƙonta, hankali kwance duk da tasan Papi ya hanata driving da kanta, Majeeder HAUWA'U MUKHTAR SULE KWALLI, ɗiya ta biyu kuma 'yar Auta ga Hajiya Sa'adatu, da Alhaji Mukhtar, Majeeder kyakkyawar gaske ce, bata da haske sosai, tana nan kalar stamiya haka, tana da hanci mai stayi da ƙaramin lip's nata ja da shi, tana da idanuwa 'yan dai-dai, bata da stayi sosai haka ma jiki, ƴar dai-dai ce ita, tana da gashinta mai tsayin gaske baƙi wuluk da shi. Tana dawowa ta hauro sama ta kawo wa Hajiya Sa'adatu aikanta, sannan Hajiya ta ce ta koma ta cewa masu aiki a ɗaura girki kamun Alhaji ya tashi a bacci, a haka ta juya ta kuma faɗa musu, sannan ta shige ɗakinta ta cire kayan jikinta ta wasto ruwa ta zo ta ɗau wayanta tana lastawa, Majeeder maƙura ce a kyau da kuma sura. Alhaji sai da ya huta sosai sannan ya tashi ya wasta ruwa, palourn ƙasa ya dawo ya zauna yana kallon labarai, ƙiran layin Mami yayi suka sha firansu, yana gamawa Hajiya ta shigo palourn, waje ta samu ta zauna ta ce, "Alhaji ka faɗawa yaronka ya cire layina a blacklist, ya ɗau ƙirana ko na saɓa masa, yaro kaman ba nice uwarsa ba duk an bi an kanainaye sa, baya girmamani balle mutunta ni ko yaji tausayina." Alhaji Mukhtar murmushi yayi ya ce, "Hajiya ke ɗin ce kika nuna masa haka ai, yanzu ma idan ba ki daina wasu yawo-yawon nan ba, zan tattara Majeeder ita ma na mayar da ita gidan General tun da shi matarsa mai zama ce, tasan mutuncin aure, ko kuwa na auro wata sai ki ci-gaba da halinki." Baki na kumfa Hajiya ta yunƙuro cikin haushi da kishi ta ce, "Babu ubanda ya isa ya ɗauka mini yarinya, idan wancan nayi shiru to wannan ba zan yi ba, kuma ba'a haifi uwar shegiyar da za ta haifa mini kishiya ba, baka isa ba, kuma ni halina lafiya lau yake atou." Murmushi kawai Alhaji yayi ya ci-gaba da kallonsa, shi Alhaji haka yanayinsa yake, shi mutum ne da kamun kaga fushi a fiskansa to za'a ɗau dogon zango, yanayinsa ke sanya Hajiya Sa'adatu yaudaran kan ta tana tunanin ko ta mallakesa ne. Hajiya kuma cigaba da yin nata surutun tayi kaman wacce aka kunnata, har dai ta gama ta gaji tayi shiru, Hajiya Sa'adatu irin matan nan ne masu kuɗi, marassa mutunci, masu wulaƙanci, ita ko yaranta ba su da lokacinta balle mijinta, gaba-ɗaya tunaninta akan business nata ne, kuma saboda haka ne ta stayar da haihuwanta wai yara biyu sun ishe su, kada ta stufe ko su hanata kula da harkokinta, karshe ma zuwa tayi aka cire mata mahaifa Alhaji bai sani ba Kwana biyu tsakani, Alhaji ya shirya ya tafi Russia kuma zai yi sati biyu kamun ya dawo, yana tafiya washe-gari Hajiya Sa'adatu ta ɗaga ƙafafuwanta ta tafi Dubai, sai da ta yi kwana uku sannan ta dawo, kuma bata sanar da Alhaji ba, Majeeder dai tana gida, daga ɗaki sai ɗaki, sai kuma driver ya kai ta makaranta idan ta dawo ya kuma kai ta islamiyya, inda a can ne ma suka yi musabaƙa, har Alhaji Mukhtar ke bawa Banafsha labari lokacin da ya kai ta school. Alhaji sai da ya kwashe sati biyu casss, sannan ya dawo, ranan ya samu Hajiya Sa'adatu sun fita da wata ƙawarta, Hajiya bushira sun je akan batun siyasar da Hajiya bushira ke ƙoƙarin stayawa takara, Alhaji ya riga ya saba da halin abarsa, shiyasa kawai ya share ya zauna, ko da ta dawo bai ce mata komai ba. ⭐⭐ LAGOS Banana island Anguwa ne na shegun ƙasa, manyan a ƙasa ba iya Lagos ba, anguwan sai wane da wance, ba ko wani laga-lagan me kuɗi ke mallakan gida a wajan ba, sai wanda ya cika cikakken babban ƙusa, fili mai araha a wajan, iya fili babu gini, arahansa shi ne 10billion, a hakanma da ne lokacin da duniya ke zaune shiru ba yanzu da komai ya tsaya da ƙafafuwansa ba. Wani gida ne wanda ya haɗu ya gaji da haɗuwa, kusan a street ɗin babu irinsa wajan haɗewa, Arnen haɗaɗɗen gida ne na gani na faɗa, kana ganin gidan kasan da starinsa da komai daga ƙasar waje ne, sai dai masu ginawan dole yan Nija ne, domin idan ana neman 'yan baiwa waɗanda suka san kan gini duk iya staruwansa to sai baƙaƙen fata, turawa masu jan kunne barsu dai kawai da iyayi, Nigeria my country. Tsayawa tsara yanda wannan haɗaɗɗen Arnen gidan yake, to tabbas ɓata baki ne da cin lokaci, dan sai mu cinye page's a abu ɗaya, tun daga wajen gidan har ciki sojoji ne kaman wanda gidan barikin sojijine ba gidan mutum ba, kai kawo sojojin ke yi kaman masu yin Safa da Marwa, Uwar batoorl ta nufi cikin haɗaɗɗen ginin dan kwaso labari sai taji iska na neman ka da alƙalaminta, a ɗari ta ɗago, da mamaki nake kallon jirgi ne na sojoji ke shawagi a saman gidan, can kuma sai ga wani ya fito a jirgin kaman zai diro, amma hannunsa riƙe da igiya har sai da ya sauƙa a cikin gidan, sannan ya sake igiyan, masu jirgin suka janye suka yi gaba, wannan bawan Allah na juyowa sai da Uwar batoorl tayi suman wucen gadi. Starki da godiya su tabbata ga Ubangijin kowa da komai, wanda ba ya gyangyaɗi balle barci, Sarkin da mutuwa ta koru gare sa, Sarki mai stara halittan bawa yanda ya so, Wani haɗaɗɗen guy ne wanda a ƙalla zai kai shekaru 34 da haihuwa, kyawunsa har ya wuce misali, idan aka ƙirasa kyakkyawa ma to an mai da sa baya ne, saboda irin haɗuwansa, gaskiya Allah yayi halitta a wajan. Jikinsa ɗan dai-dai, yana da ɗan stayi da ya tafi da yanayin jikinsa, fari ne tasss ma kuwa kaman Balarabe, duk yanda ma aka yi ya haɗa jini da 'yan wata ƙasar bayan Nigeria, idanuwansa dara-dara kaman na mace, wanda na tabbata duk wanda ya gansa zai so ƙara ganinsa ko dan idanuwansa, daga gani ba ƙaramin rububi mata ke yi akan idanuwan nan ba, yana da hanci mai stayin gaske kaman na Majeeder, yana da ɗan ƙaramin baki, lip's nasa ja kaman na Majeeder, matuƙar kama suke yi da ita, banbancinsu kawai launin fata, da ɗan gemunsa dai-dai kaɗan, da sajensa dai-dai, sannan ga wani irin arnen kisto a kansa, da gashin sa da yayi kama da na larabawa, da aka kista kuma yayi kaman na turawa masu baƙin gashi, wata kafurar aski aka masa sannan aka kista gashin nasa, mai tsayin gaske, sanye yake cikin kaya mai kama da up&down, wanda zip ake buɗewa a gaban daga sama har ƙasa a saka, rigan haɗe yake da wando, kuma kayan irin na sojojin sama ne, ƙafansa kuwa sanye yake cikin sandal's wanda shi ɗin ma na sojoji ne, ga wani uban headphone a kunnensa shi ɗin ma irin kakin sojojin sama ne kalansa. Tunda wannan haɗaɗden guy ɗin ya sauƙo daga jirgi ta sama, shikkenan duk sojojin cikin gidan suka sha nistojin, suka nistu sai zuru-zuru kawai suke yi, amma tun sauƙansa duk suka sara masa suna faɗin, "Welcome Sir." Wannan gayen bai ko ɗaga idanuwansa ya kalli mutum ɗaya a cikinsu ba, cikin isa da ji da kai yake tafiyarsa ta jarumai har ya shige katafaren gidan nasa, ya Ilahi! Fan's ga wata dalleliyar palourn ma wacce koman cikinta ordern waje ne, colorn komai na babban palourn blue black ne da kuma light arsh, komai yaji zam-zam, komai ya haɗu ya gaji da haɗuwa, cikin isa yake tafiya har yanzu headphone ɗin na kunnensa, sai gyaɗa kai yake yi har ya haura ɗan step's ɗin, ya tura wani kyakkyawan ƙofan glass ya shige ciki, da wani makeken gado na fara tozali, gado ne wanda mutum goma ma sai su kwanta lumui lafiya, ba dan irin starin gidansu na can ba, a nan arewa kam babu irin ɗakin. Yana shiga ya cire kayakin jikinsa duka ya bar boxers kawai, ya tura bathroom ya shige, sai da ya wásta ruwa ya fito ɗaure da guntun towel sannan na kuma ganin irin haɗewansa, jikinsa daga bayansa zuwa hannayensa duk tatoo ne, ƙirjinsa mai cike da gashi ne kawai babu tattoo, kuma ba ƙaramin kyau zanen ya masa ba, gaban mirror ya je ya danna wani abu, sai ga mayukan shafawa iri da kala, yana shafawa ya maida, ya kuma danna wani turarukansa suka fito, sai da ya gama shafe-shafensa staff ya yiwa wannan kiston kan nasa mugun gata, sannan ya wuce wajan kayakinsa ya ciro 3quater da armless duka na sojoji ya saka abinsa, ya kuma feshe kansa da turare kaman ba lau ba, sannan ya ɗau wayoyinsa ya fito a ɗakin, da kansa ya shiga kitchen ya haɗa dan abu dai-dai mara nauyi, wanda zai iya ci ya kawo dinning da kansa ya ci, yana gamawa ya tashi ya koma palourn sa ya kwanta tare da kunna TV ya kamo tashar turawa da ake romantic films, wanda matan suke yawo kusan tsirara, bai wani mai da hankali sosai akan TV din ba, ya fidda wayarsa ya shiga dialing layin abokinsa. Ana ɗauka a ɗaya ɓangaren aka ce, "Assalamu'alaikum! Kunga ƴan iskan gari, manyan gari, arnan gari, masu certificate a Nigeria da ƙetaren Nigeria." Murmushinsa mai tsada ya saki tare da shafa kiston kansa ya amsa sallaman, sannan ya ce, "Abeed ka daina kafurta ni, ina musulmi ɗan musulmi, jikan musulmi, haihuwan musulunci." Abeed ma a nasa ɓangaren murmusawa yayi ya ce, "Chief of the air staff Bunayd (CAS bunayd), manyan ƙasa ya aka yi? Da alama kana Lagos, yaushe ka dawo daga New York ɗin?" "Ko 1 hour ban fi da dawowa ba, ya kake ya kowa da kowa? Ya kamilarka?" Dariya Abeed yayi ya ce, "ka ce kada a ce maka arnen ƙasa, ga shi kana cewa wai ina kamila ta, kai fa kaƙi ganewa CAS, hadisi ne fa guda ya ce Adduniya mata'un wa...." Bunayd dakatar da shi yayi ya ce, "wa khairu mata'u ha, mar'atussaliha." Abeed ya ce, "ɗan iska, ai nasan ka sani, take saninka kake yi, wai kai ka dage baka son kamilar mace, to kai baka son mar'atussaliha ɗin kenan? Ka fi son wacce za ta kashe ka a tsaye ko." Murmushi mai tsada Bunayd ya saki ya ce, "Kai baƙon duniya ne tukunna har yanzu, baka san rayuwa ba Abeed, kaƙi wayewa kwata-kwata sam, ga ka dai ka zaga duniya amma shiru kakeji, diɗim kaman an shuka dusa", ni dai Uwar batoorl da mamaki nake kallon wanga haɗaɗɗen gayen, ganin har da ƙarin hausa ya iya, ba iya hausan ba, mutumin da idan ka kallesa ka ɗauka ko kunnen uwarsa aka ce da hausa ba zai ji ba. Abeed a ɗaya ɓangaren ya ce, "To nidai bana fatan shigowa wannan irin taka rayuwan, ina cikin rayuwa kana faɗin bansan rayuwa ba, to kai ba ka son kamammiyar mace saliha, me mastalanka? kaƙi maganan aure gida da waje, ko ƴan iskan turawan da suke maƙale maka kaƙi su wai iskancinsu yayi kaɗan, su ma basu san rayuwa ba tukunna, duk irin fitsarar su ai dai kasan ko karuwa bata kai matan turawa iya iskanci ba, mutanen da suke yin BF kuma me ya rage musu." Bunayd taɓe baki yayi ya ce, "Ba za ka gane ba Abeed, ka riƙe kamilarka, sunan wani wai saliha, to riƙe abarka, ni tsagerar ƴar iska cikakkiyar nake son na samu tukunna, idan na jarrabata naga ta gane rayuwa tasan ta kan harkan caja Palace, da kuma cinikin ka saya ɗaya a baka biyu kyauta, to normal ne ba mai hanani aurenta sai Assamadu." Abeed guntun tsaki ya ja ya ce, "Yanzu haka ga shi ina jiyo screaming na mace da alama dai film ɗin naka kake kallo na yan iska, kai kaƙi kallon Blue Film amma kana ganin irin waɗannan, kaƙi cin biri ka ci dila, wai ba cinyar ba ƙafan baya, to me marabin dambe da faɗa?" Murmushi Bunayd yayi ya ce, "Kai yaro ne, kanka yayi kaɗan ko na banbanta maka ba za ka gane ba, anyway ni dai tantiriya wacce ta san ta kan harkar caje Palace nake nema, ina samu kuwa wuff da ita zan yi, kullum cikin kwaso shoki a Palace zan kasance, amma kaga kamilallun nan, daga first night sai a ce sai ka yi week kana barinsu su huta, kuma a na ɗan stallake kwanaki, amma kaga ina samun stagera, tantiriya wacce tasan rayuwa tasan duniya, wacce za ta iya laying nawa a down ta mini full cherge to komai dai-dai, ni ina ƙulla abota da Palace to ko period haka zai ganni ya bar ni, saboda ba ma ƙyamar jinin nake ba, a haka sai na caje Palace hankali kwance, duk normal ne, saboda mugun yin Palace da nake to wannan jininma yinsa nake irin overn nan hundred percent ma kuwa." Dariya Abeed ya kwashe da shi kaman mai ƙaramin hauka, ya ce, "daɗina da kai ka iya surutu akan wannan Palace-palace da ka addabi mutane da shi, in iskancin kake ji da tantiranci na tantiraye cikakkun ƴan iska, ai sai ka ƙira sa da asalin sunansa." Murmushi Bunayd yayi ya ce, "Man baka san rayuwa ba, ai yanzu an waye, duk dirty talks ɗin nan shirme ne, idan ka ce Palace ya kaji yanda abin ya bada citta? Ai normal kawai ako ina a bajeta kawai duk wanda ya gane normal, wanda bai gane ba ma can da yawarsa." Dariya Abeed ya dinga yi, shi dai Bunayd sai dai murmushi mai shegen zafi kawai, maganganun ma kaman ba shi ya ke furta su ba, a haka suka dinga wayarsu cikin nishaɗi har suka yi sallama, Bunayd ya kashe wayansa ya kalli TV dai-dai lokacin wani bature na sucking Palace na wata babe tasa, murmushi Bunayd yayi ya ce, "ai ku ne duniya, ku ne sanin duniya, Allah nima ka bani tantiriya ta wacce zan wanke mata Palace na ɗauraye shi, na lashe shi, na busar da shi, na masa full cherge." Alwala yayi tare da yin Sallah sannan ya kwanta a makeken gadonsa, ba jimawa bacci yayi gaba da shi, da mamaki dai nake kuma kallon CAS Bunayd, ganin namiji da shi amma birgima yake yana juyi a ƙaton gadonsa, sai tale ƙafa kuma yake kaman abin ba dama. Shi ne bai tashi bacci ba sai can yamma, yana tashuwa da addu'an bacci a bakinsa ya ɗaura alwala, karatun Alkur'ani mai girma yake rerawa, subhanallahi fan's wannan CAS ɗin da abin mamaki yake, kunji kira'a kuwa kaman limamin Saudi ke rerota, sai da lokacin Magrib tayi sannan ya aje ƙur'anin, ya tashi yayi sallahnsa, nan ma komawa yayi ya zauna yana azkar yana jan carbi, shi ne bai tashi a wajan ba sai da yayi isha'i, yana idarwa ya miƙe tare da fitowa cikin gidan nasa, wanda yake da haske tarr ko ta ina kaman da rana ne, ga kuma sojoji na kai komo kaman masu jiran ko ta kwana, yana tsaye yana shan fresh air ƙira ya shigo wayansa, ɗauka yayi ganin General ne, cikin yanga yayi sallama, General ya amsa tare da cewa, "kana gidanka ko?" "Yes General." Jinjina kai General yayi a nasa ɓangaren ya ce, "Okay! Ka zo gida yanzun nan." Ɓata fiska CAS yayi kaman wani ƙaramin yaro ya ce, "Toooo! An coming." General murmushi yayi tare da kashe wayansa, CAS Bunayd kuwa cikin gidansa ya koma, wanka ya kuma fesawa ya saka wani armless ɗin da 3qauter, feshe turarensa yayi ko ta ina sai ƙamshi kawai yake yi na fitan hankali, yana fitowa wasu sojoji da gudu-gudu suka ɗauko motoci kusan guda goma, CAS Bunayd kallonsu yayi ya taɓe baki fiskan nan a haɗe, kaman an haɗo baƙar hadari, da mamaki na ce ashe dai mutuncin da fara'an wa iya abokinsa ne, waɗannan sojoji Aradu suna ganin rashin mutunci wajan wannan Bunayd ɗin, cikin isa ya ce su ƙyalesa zai je shi ɗaya, amma suka ce ina, saboda baya son dogon magana da su, motan da ke tsakiya wanda ya fi ko wanne haɗuwa suka buɗe masa ya shiga, duk da gudu-gudu suka shige nasu motocin, a saba'in suka bar cikin gidan, motoci biyar a gaban nasa, biyar a bayan nasa, sai stula gudu suke a cikin garin Lagos, gudu na Allah stine uwar mai ƙarya, domin ba laifi su ma sojojin, suna fesa rashin mutuncinsu a kan kwalta, idan ka sake ka kusto gabansu to rip gare ka, dan kaman ba su da birki, ga mugun gudun stiya, shi dai CAS Bunayd yana hakimce a bayan haɗaɗdiyar motansa, sai lasta wayansa yake hankali kwance ko ɗago kai baya yi, kuma daman wannan al'adansa ne, shi abinda yake gabansa kawai yake yi, in za ka shekara staye a kansa ko a gefensa, sai ya shekara bai dago ya kalleka ba, ko kuma bai juyo ba. Victoria Island suka nufa, nan ɗin ma anguwan wasu manyan kusoshin ƙasa ne, anguwan manyan yan kasuwa, manyan masu kuɗin ƙasa, da kuma sojoji da ƴan siyasa. A gaban wani katafaren kantamemen gida suka buga wata mahaukaciyar horn, kaman za su tashi garin Lagos da bala'i, wannan gidan ma sojojin ne ko ta ina kaman kayan banza, ana buɗe musu, suka danna hancin motocinsu ciki, Masha Allah! Wannan gida ma ta haɗu ta tafi da zuciyata, ba dan gidan manya ba ne to da tabbas motocin CAS Bunayd ba za su samu mastugunni ba, amma da yake wannan gidan ma ya amsa sunansa, to kaman ba motoci goma sha bane suka shigo, kuma akwai wasu arnun motocin a gidan ma, waɗanda suke mallakin mai gidan. Suna gama parking, wani soja ya zo da gudu ya buɗewa CAS Bunayd ƙofa tare da ƙamewa ya sara masa, amma bawan Allah sai da ya kusa mintuna biyar a cikin mota sannan ya jeho ƙafa guda a waje, can da ya gama iyayinsa sai ya fito gaba-ɗaya, wannan karon har da glass ya maƙalawa fiskansa da babu annuri, cikin isa yake takunsa na ƙasaita, hannu guda a aljihu hannu ɗaya riƙe da wayansa mai stadan gaske na yayi, ga kuma uban headphone a kunnensa, a haka ya shiga gidan da sallama kansa akan wayansa, ba ruwansa da an amsa sallaman ko ba'a amsa ba ya haura sama direct, a palourn sama ya samu General a kwance Matarsa Hajiya Huraira tana masa tausa, duk da shigowan CAS Bunayd bata bari ba, ci-gaba tayi ta aikinta tana sakarwa yaron nasu murmushi. Waje CAS Bunayd ya samu ya zauna, cire glass nasa yayi, sannan cikin girmamawa da maganarsa ta yanga ya ce, "General barka da gida, Momsee sannu da aiki." Hajiya Huraira wacce suke ƙira da Momsee, tana murmushi ta ce, "Yauwá, sannu Bunayd, fatan ka dawo lafiya?" "Alhamdulillahi Momsee" ya faɗa yana mai ɗan kishingiɗa. General ya ce, "My Man, yaushe ne ka dawo?" Cikin shagwaɓa kaman ƙaramin yaro ya ce, "Yau na dawo." "Good! Sannu da hanya Man, wai me yasa baka son zama anan gidan ne? Ka yi gida a gefe ka koma can da zama menene damuwanka? Ko dai rashin ji kake shukawa?" Faɗin General idanuwansa akan Bunayd. CAS Bunayd shafa kiston kansa yayi dan ya fahimci nufin General na cewa wai ko rashin ji yake shukawa, murmushi yayi mai stadan gaske ya ce, "General ni ba wani abinda nake shukawa, just small boy like me ai babu abinda zan iya yi, ba mace ko ɗaya a gidana, kuma wasu ayyuka nake yi, amma zan dawo, nima ba daɗin zaman can ɗin nake ji ba." General yana kallon Bunayd cikin soyayyan da yake masa ya ce, "Kai ne small boy? Anyway shikkenan, I trust you, nasan ba za ka shuka rashin ji ba, yanzu dai ko baka kammala aikin ba, ba inda za ka koma, ka dawo kenan, bana son zamanka kai kaɗai a gida." Haka ya ƙara marairaicewa kaman ɗan goye ya ce, "General zan dawo da gaske fa", magiya Bunayd ya dinga yi da gaske, sannan General ya amince akan idan ya gama ya dawo, sosai General yake ƙaunan Bunayd, shi ya sakalta shi, ya shagwaɓa shi. General ya ce, "To kai ka ce small boy ne kai, yaya kuma ya ce aure za kayi, dan kada ka shuka rashin ji, dan nasan dai ba lalacewa za ka yi ba, sai dai shuka rashin ji ɗin." Murmushi CAS Bunayd yayi ya ce, "General ka ƙyale Sir, ni har yanzu gaskiya banga wacce ta mini ba." General ya ce, "Amma dai kasan halin yaya ba, staff zai aura maka wata, gwanda kawai ka nemi nistasttiya tun wuri ku dai-daita, ni bana son a maka abinda baka so." CAS Bunayd ɓata fiska yayi ya ce, "General to gaskiya da ace Sir yasan irin macen da nake so, ai ba mastala ya zaɓa mini, amma ga shi kai ma da muke tare kana cewa nistasttiya balle kuma Sir, ai sai ya ce shi kuma kamila mai kwana da hijabi tana guma Palace zai nema mini, gaskiya a barni na nemi irin wacce nake so." General cikin soyayya da lallashi ya ce, "To wacce irin mace kake so my Man? Ka ce ba nistasttiya ba, kuma ba kamila ba, Ustaziya kake so kenan?" CAS Bunayd ji yake kaman ya ƙwala ihu dan taƙaici, kaman zai yi kuka ya ce, "General ni ko ɗaya ba su nake so ba." "To wai wacce irin mace kake so?" "Gaskiya General ni bana son mata masu saka hijabin nan, ƴan ƙauye ne, gaskiya ni banason nistasttiyan mace." Da mamaki General da Hajiya Huraira (Momsee), suke kallon Bunayd, Momsee ce ta ce, "To Bunayd wace irin mace kake so? Kowa na fatan samun nistasttiyan mace amma ka ce ba haka ba." "Momsee ni nafison mace wacce ta waye tasan rayuwa, tasan duniya, amma nistatststun nan basu san kan rayuwa ba, basa bada Palace yanda ya kamata." General ya ce, "shi kuma Palace ɗin menene? Ai mace nistasttiya ita ce jin daɗin duniya." "General ni nafison wacce take nan tantiriya-tantiriya, ko gantalalliya-gantalalliya haka nan, ko stagera-tsagera ko kuma wayayyiya wacce dai ba kamila ba, wacce dai tasan rayuwa, nistasttiyan nan cutan ta zan yi, kaga ni ba nistastte bane, kuma ni Soja ne, nistasttiya ai sai malamin islamiyya, ustazu." Momsee dariya kawai ta yi, shi kuwa General sake baki yayi ganin ikon Allah, ganin da gaske CAS Bunayd ya dage shi iya gaskiyansa yake faɗa, abinda yake so yake faɗa, ikon Allah, da mamaki ya ce, "ubanwa ya ce maka kai ba nistastte bane?" Bunayd ya ce, "Abeed ne ya faɗa General." Girgiza kai kawai General yayi, tunda yasan Abeed kuma ya san waye Bunayd ɗin da rashin jin sa, kawai soyayyan da yake masa ya saka yake lallaɓasa, rarrashinsa ya dinga yi amma ya dage firr shi baya son nistasttiya, in kuma Alhaji zai sama masa wacce yake so, to ya basa zaɓi, shi normal ne kawai, ai damuwansu yayi aure ne, to zai yi kawai a samu kalar wacce yake so, General dai kama haɓa yayi yana ganin ikon Allah, amma tunda dai ya amince zai yi auren da sauƙi, kuma daman hakan na ɗaya daga cikin abinda yasa yake son sa sosai, Bunayd baya musu da su ko kaɗan, kuma yana jin maganansu yana musu biyayya, halayyansa masu kyau ne, dan ya fi ƙannensa har da matan jin magana, shi dai bar shi da abin raha, ita kuwa Momsee ba abinda take yi sai dariya, ganin Bunayd ya girma da gaske amma kuma ƙuruciya na damunsa, dan idan ba ƙuruciya ba mutun ya dage baya son kamilar mace saliha, ya ce sai gantalalliya. General ajiyan zuciya ya sauƙe ya ce, "To daman ma babban abinda ya sa na ƙira ka, ba akan ka dawo bane, dan nasan muddin baka yi niyan dawowa ba tuni ka kanainaye ni da magana na ƙyaleka, ga shi kuma na haƙura dan dole, Man kai kam ai mace bata isa ta maka daɗin baki ba, Allah shirya mana kai." CAS Bunayd na murmushi ya ce, "Ameen Ya Rabbi my General." General sai da ya dara kawai ya girgiza kai ya ce, "akan maganan ƙannenka ne, da farko Suhail na kai sa makarantar sojoji shi ma ya gado ni, amma yaron nan ya gudo haka na kylesa, aka tura sa Turkish ɗin da yake so, ya karanto duk shirmen da yaga dama, yanzu kuma Nabeel ya ɗau ƙafansa, dan tsabar yaran nan duk sun mai da ni abin wasansu wai shi ɗin ma yaro da shi yana cewa ba zai je ba, baya so, bansan mene mastalansu da aikin Soja ba, yara duk basa kishin kansu balle ƙasar su, ba za su tsaya su kare ƙasar su yanda muke fafatawa ba." Bunayd murmushi kawai yayi ya ce, "General wallahi ba ko kaffara, Suhail ne ya zuga Nabeel wai wahala ake, amma ba komai zan yi wa Nabeel ɗin magana." "Good boy! Allah muku albarka duka my Man, idan kuma yaƙi ji ka kai sa guard room ba ruwana" faɗin General yana murmushi. CAS Bunayd ya ce, "Ba za'a je ga guard room ba ma General." Dariya General yayi ya ce, "Daman nasan haka za ka ce ai, tunda ka fi kowa son ƙanne a duniya, duk kai ma ka sakalta yaran nan, amma dai tunda suna jin magananka da sauƙi, ni na rasa ya ake suke storonka ma yanda kake buɗe musu haƙorankan nan." Murmushi kawai CAS Bunayd yayi bai ce komai ba, ya shafa kistonsa yana lumshe idanuwansa kaman mai jin bacci. Momsee ganin Bunayd na ƙoƙarin yin bacci sai tayi murmushi ta ce, "To muje a ci abinci dama kai muke jira." Duk miƙewa suka yi suka sauƙo dinning na ƙasa, kowa ya samu waje ya zauna, yaran mata ne guda uku suka fito, kyawawa da su masu kama da General, kuma daman Bunayd da General yake kama shi ma, ɗaya a cikinsu ba za ta haura shekara sha tara ba 19 mai suna Ramla, sai ɗaya ba za ta haura 17 ba ita kuma sunanta Suhaila, sai kuma autar cikinsu da ba za ta haura 14 ba mai suna Nabeela, duk a niste suka gaishe da Bunayd ya amsa fiskan nan a sake yana musu murmushi, General ne yayi magana ya ce, "table manners, kowa ya ci abinci ayi shiru." Duk stitt suka yi baka jin ƙaran komai, sai na spoon da plate da suke karo, yayin da CAS Bunayd kuwa rabin hankalinsa ke kan wayansa yana sakin murmushi. ⭐⭐ Banafsha suna dawowa daga wajan musabaƙa aka sallami kowa ya koma gida bayan an ƙara ƙarfafa musu guiwa su dage, tunda sun ga yacce rashin ƙwarin guiwa ke sa wasu faɗuwa, babu confidence. Malam Abbo ne ya biyo su Banafsha yana taka musu, yana ƙara basu shawarwari yanda za su yi karatunsu hankali kwance ba tare da yawan idanuwan jama'a a kansu ya dame su ba, ko ya hana su yin nasara, su Umaima dai suna ta sauraronsa har ba su ankare ba suka fara hango gida, Malam Abbo ma na farga ba ashe ya biyo su har gida, kuma tun daga nesa Umaima da Banafsha suka hangi Ya Danish a ƙofan gida kuma ya kallesu. Malam Abbo sallama ya musu zai juya, sai Banafsha ta langwaɓar da kai ta ce, "Malam ba ka faɗa mana abinda ya hanaka zuwa ba, in rashin lafiya ne ai sai mu dage da addu'a, Allah bawa malaminmu lafiya." Umaima duk ta sture ko sauraran su Banafsha bata yi, kuma ta kasa tafiya tabar Banafsha, ga shi Ya Danish ya zuba musu na mujiya ko ƙiftawa ba ya yi, kuma fiskan nan a haɗe, kana gani kasan yau akwai bala'i. Malam Abbo yana murmushi ya ce, "Na ɗan yi tafiya ne urgent zuwa Borno, afuwan ko Malama Faɗima." Banafsha murmushi ta sakar masa mai rikitasa ta ce, "tunda Malam ya dawo lafiya Alhamdulillahi, sannu da gajiyan hanya, gobe kada a mance mana tsarabanmu Malam", ita fa Banafsha duk saboda Ya Danish ya ƙulu take yi. Malam Abbo da ya susuce, murmushi kawai yake sakarwa Banafsha kaman ba lafiya ba, har ya buɗe baki dan faɗa mata akwai maganan da yake son faɗa mata, amma sai ya fasa kawai ya dake, ya musu sallama ya juya, zuciyansa cike da wani irin ƙaunar ɗalibarsa Faɗima. Banafsha da gangan ta staya tana yiwa Malam Abbo bye-bye, duk da ya riga ya juya, amma yi take dan Ya Danish, har da ɗaga hannu sama ta yi alaman love, Umaima da ta gaji da haukan Banafsha sai wucewa tayi ta ce, "Sai kin iso, tunda ba ki san ruwan da ke gaban mu yana jiranmu ba, yau nasan nidai na gama yawo na kaɗe, Ya Danish zai targaɗa ni. Banafsha na murmushi ta juyo, daga inda take ta harari Ya Danish sannan ta bi Umaima da sauri tana faɗin, "jirani Umaimaty, zan je wajan Ummu." # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKI NE Hareeyh (Uwar batoorl)🤣 Masu Sharhi sun ƙare, dole na bawa kai ka page, nima na ɗana ladan typing. اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 41 _ 45 Umaima tuni tayi nisa da tafiya ko jin Banafsha bata yi. Sai da suka iso dai-dai wajan su Ya Danish sannan Banafsha ta ce, "Umaima na fasa binki." Ai da sauri Umaima ta ƙankamo hijabin Banafsha ta ce, "wallahi kin yi kaɗan Masoyiya, tunda kika ja mana ruwa dole ruwan nan ya dake mu tare, ba inda za ki je." Banafsha na danne dariyanta, suka gaishe da su ya Farooq, Umaima ce kawai ta gaishe da Ya Danish, amma Banafsha ko kallon inda yake bata yi ba, nunawa tayi ma kaman bata san da halittansa a wajan ba, shi kuwa Danish aikon masifan da ya ƙulla ko gaisuwan Umaima bai amsa ba, buri yake kawai Banafsha ta shiga gidansu, yau sai ya seta mata hankali ya gyara mata wajen zama, ga shi Abbaa ba ya gida balle ya ƙwace ta, dan cike yake da haushin abinda ta masa ranan, kuma tsaff ya shirya muguntan da zai mata, ta yacce ko da kuɗi aka haɗa ta akan ta ƙara faɗa masa magana ba za ta iya ba. Umaima haka ta maƙalƙale Banafsha sai da suka shiga gidan tare, suna shigewa Danish ya mike stamm! Ya rufa musu baya yana sakin murmushin mugunta, cikin dabara ya faɗawa su Farooq bari ya ɗauko abu a ɗakinsa ya dawo. Yana shiga ya samu har sun shige cikin gida, ƙwafa yayi tare da sakin murmushi ya wuce part nasu na maza da yake ta bakin ƙofa yana jiran fitowanta. Umaima suna shiga cikin gidan ta saki hamadala tare da cewa, "To nidai na stira, saura ke mai fita ki koma gida, Allah shiga tsakaninki da masifan da ke bakin ƙofa yana jiran fitowanki." Banafsha Murmushi kawai ta sakar wa Umaima, ta nufi ɗakin Ummu, amma a bakin ƙofan suka kusa yin karo da Nana ta ce, "Banafshaty, ai Ummu ta bi Abbaa sun je asibiti dubiya tun ɗaxu." Umaima ma fitowa tayi a ɗakinsu ta ce, "sorry masoyiya mancewa nayi ban faɗa miki Ummu bata nan ba, duk storon Ya Danish ne ya cika ni, matar abokin Abbaa ce babu lafiya، shi ne suka je gaisheta a asibiti." Harara na aikawa Umaima dan taban haushi, storonsa sai ka ce ya zama wani mala'ikan mutuwa, ba tare da na saurareta ba na juya zan fice, Umma da fitowanta ɗaki kenan, ƙwafa tayi ta ce, "Idan na kuma ƙara ganinki a cikin gidannan ni nasan abinda zan miki, yarinya gaba-ɗaya bata da zuciya, wato har gida kike bin kabeeru ko? To kuwa zan baki mamaki idan kika ce za ki ɗaura shegun fistararrun idanuwanki akan yarana, ki ƙare can ke da karuwar uwarki, kuma idan ma shanyewa yarinyata zuciya kika yi take binki a baya kaman bindi, to ki sani ina dai-dai da maitanki, idan baki ƙyale mini yara kin fita harkansu ba to ba shakka zan saɓa miki." Umaima ta buɗe baki za tayi magana sai Umma ta kwashe ta da mari, saurin juyowa nayi rai na a ɓace saboda maganganun Umma, idanuwana akan Umaima na mata alama da ido kada ta ce komai, matar babban yaya ce ta aiko mini da harata tare da yin staki ta ce, "Wallahi idan baki fita harkan mijina ba sai na miki illa, shegiya, ƴar iska, ƴar karuwa..." Kamun ta rufe baki tuni na dira gabanta na kwasheta da maruka biyu ba ruwana da cikin jikinta, amma kamun na ɗago tuni Umma ta kwashe ni da marin nima ji kawai kake tassss! tasss!, cikin masifa Umma ta ce, "Dan uwarki har kin isa ki taɓa mini surka yar gidan mutunci? Kina ƴar karuwa, ƴar shege" Ba tare da na tankawa Umma ba, na kuma ɗaga hannuna na kwashe matar yaya babba da maruka, zuciyana na tafasa na ce, "ki bari manyan da babu yacce na iya da su suyi, dan su zan iya ƙyale su, idan ma basu riƙe girmansu ba to ni san basu mastayinsu, amma ke kika ce za ki shiga stabgata zan iya fige miki gashin mugun waje, ni ɗin nan ban da kirki ban da mutunci, kibar ganin wasu nayi ina shiru ki ɗauka ke ma za ki ci banza, wallahi kika masta a lamarina sai na saka zuciyanki ta buga, ƴar iskan kai na ce ni ɗin nan, mijinki da ya mini to ko kallonsa ba za kiyi ba balle ya aure ki." Umma kuwa jin abinda na faɗa, a fusace ta iyo kai na tana masifa, amma sai Umaima ta tare ta tana kuka tana cewa, "menene haka Umma? Dan Allah ki bari, da ƴar cikinki kike haka, wallahi idan Banafsha ta rama marin da kika mata ba ruwana ba zan ji zafi ba ke kika nema...." Bata rufe baki ba amma ta hankaɗata gefe ta iyo kai na, matar yaya babba kuwa da taji mari tuni ta zauna daɓas da cikinta a ƙasa ta kasa yin magana, ga haushina ga kuma shakka na. Wani irin kallo na yiwa Umma tun kamun ta iso gareni, sannan na juya, sai ji na nayi na ci karo da mutum, idanuwana a rufe ban damu da wa nayi karo ba na ci gaba da tafiya, sai ji nayi an riƙe hannuna anyi baya da ni, a hasale na ɗago jajayen idanuwana cike da masifa, amma sai tozali nayi da yaya babba, rai na ƙara ɓaci yayi na ƙwace hannuna na juya, bi na yayi yana cewa, "kiyi haƙuri Banafsha, kada ki tafi a haka.." Umma cikin ɓacin rai ta ce, "kabeeru idan ka kuma taku ɗaya sai na stine maka, dan Ubanka me haɗin ka da ita? daman gaskiya Hindatu ke faɗa mini kenan? Tunda ga shi har haƙuri kake bata, bayan rashin kunyar da ta mini, ta kuma mari matarka da juna biyu a jikinta." Babban yaya stayuwa yayi rai a ɓace bai cewa Umma komai ba, dan shi Banafsha ta masa dai-dai ko me ta musu su suka nema da kuɗinsu, kwafa yayi yana bin matar sa da mugun kallo, domin kusan duk abinda ya faru akan idonsa ya faru, kuma yasan laifinta ne, daman tun ranan ya fara ganin take-takenta, Umma ma harara ta aika masa da shi ta ce, "idan ka kuma yiwa yarinyar nan magana sai nayi mugun ɓata maka rai wallahi." Umaima da ke yashe a gefe can ta buge hannunta a jikin kujera har hannunta ya ɗan kumbura, kuka ta sanya kawai, cikin gaggawa yaya babba yayi wajanta yana duba hannun nata, tausayinta ne ya rufesa ganin har taji ciwo, dan sosai suke son Umaima yayyun nata. Ni kuwa rai na a ɓace na fito bana ko kallon hanya haka nake tafiya kaman zan tashi sama, ba zato ba tsammani naji anyi sama da ni, saboda ɓacin rai da nake ciki ko ƙoƙarin buɗe baki banyi ba balle ihu, sai dai zillewa da nake ƙoƙarin yi dan bansan wa ya ɗaga ni ba, ganin da nayi an shiga sashin mazan da ni, nan na tabbatar da mai wannan aikin, muna shiga ciki aka dire ni a ƙasa har sai da na ƙafata ta lanƙwashe ta mini zafi. Miƙawa nayi naja staki kawai na nufi ƙofan fita, dan ba sai na kalli waye bane, saboda nasan wa zai iya mini wannan aikin marassa hankalin, hijabina ya rike tare da jawo ni baya ya hankaɗa ni kan kujeran zaman mutun uku da ke cikin palourn, faɗawa nayi kai na buge bayana kuma, runste ido nayi tare da sakin ɗan marayan ƙara, sai lokacin na ɗago idanuwana na sauƙe su a kan sa, wani malalacin ɗan iskan kallo na aika masa da shi sannan na ce, "Wallahi ka fita a harkata idan ba haka ba zan iya kashe ka Danish, na tsaneka kaman yanda ka tsaneni, banason kallonka, ka dena taɓa ni idan ba haka ba zan iya illataka." Danish murmushin mugunta ya saki ya ce, "bayan kisa kiyi abinda za ki iya yi, ba dai ni kike faɗa wa maganan banza ba, to zan gwada miki iskanci irin nawa ganin idonki dan ki sani, ko a cikin kwartayenki babu sa'a na balle ke ƙaramar karuwa, har ni za ki cewa ba'a ɗan iska ɗaya sai biyu, to kuwa yau zan nuna miki irin nawa iskancin, gobe ko da kuɗi ba za ki yiwa wani ba balle ni Danish." Miƙewa nayi tare da sakin murmushi mai nuni da bai san abinda yake faɗa ba, kallonsa nayi sama da ƙasa duk da belt na wandonsa da yake ƙoƙarin cirewa amma hakan bai dame ni ba, sai ma dogon stakin da naja na ce, "Na faɗa, na kuma faɗa, kuma zan ƙara faɗa, jikin Banafsha ya fi ƙarfinka Danish, na wuce sa'ar yinka, kai mata-maza nake maka kallo, ka je a kuma maka kaciya sannan ka tunkare ni, " ina gama magana na yi hanyan fita. Wannan karon cikin zafin rai ya jawo ni ya haɗa ni da bango har sai da na buge kai na, a cikin mugun ɓacin rai ya ce, "Zan kuma gwada miki cewan nafi ƙarfinki yanzu, sai na miki kaca-kaca, sai na illataki, sai na miki abinda babu wanda ya taɓa miki irinsa duk yawon iskancinki, za ki ga mata-maza ganin idonki yau" yana gama magana cikin zafi ya ja hijabin jikina ya yage sa, saboda kada nayi ihu ya haɗe bakinmu waje guda sannan ya fara kiciniyar cire mini kayan makarantan da ke jikina, ni kuwa tunda ya haɗe bakinmu waje guda tuni wani irin storo ya ziyarce ni, banason zina, na tsani zina, bana son mai aikatasa, ko mahaifiyata babu yanda na iya da ita ne shiyasa, ita ɗin ƙaddarata ce. Abbaa da Ummu dawowansu kenan daga asibitin da suka je, da yake a waje Abbaa ya bar mota, to tun shigowansu suke jin kaman ana kokuwa a sashin su Sadeeq, har za su wuce sai Ummu ta ce su duba dai su gani ko lafiya, Abbaa ba musu suka juya suka nufi ƙofan palourn samarin, suna isa kuwa suka jiyo kaman shessheƙan kukan mace, da sauri Abbaa ya tura ƙofan. Kiciniyar ƙwacewa na fara yi, ina son nayi ihun naiman taimako ganin ya Danish da gaske yake, amma yaƙi bani daman hakan, ba shan bakina yake ba amma ya rufe mini baki da nasa, nan muka fara kokawa da Ya Danish, da yake ya fi ƙarfina sai samun galaba yake a kai na, har ya kai ni ƙasa ya danneni, kaman yanda zuciyana ke buganawa nakan iya jiyo nasa sautin bugun zuciyan tunda ƙirjinmu ya haɗe waje guda, yana ƙoƙarin zare wandon jikina kawai aka banko ƙofa aka shigo, waye za mu gani? Abbaa ne da Ummu, cikin hanzari Abbaa ya zo ya janye ya Danish tare da kwashe shi da maruka, Ummu kuma ta ɗaga ni tana kuka ta ja hannuna, bata koma cikin gidan da ni ba ta yafa mini ɗankwalinta hannunta cikin hannuna tayi gidanmu da ni, nima a nawa ɓangaren hawaye kawai nake yi dan nayi mugun storata, stanar Ya Danish ya ƙara rufe ni, nayi nadaman sanin wannan gidan nasu a rayuwata, tuna har ya haɗa bakinsa da nawa sai kawai na fashe da kuka na faɗa jikin Ummu dai-dai mun shiga haraban gidanmu. Abbaa kuwa ba abinda yake yi sai aikin marin ya Danish yana faɗin, "Ni za ka tozarta Danish? Ni za ka wulaƙanta a garinnan? Yarinyar mutane za ka yiwa fyaɗe dan baka da kirki? To wallahi gwanda na kashe ka na huta da ina gani na bari ka ƙetawa yarinyar mutane mutunci, abun kunya za ka jawo mini ina zaune lafiya." Ya Danish ko ajikinsa maganan Abbaa bai damesa ba, shi haushi ɗaya yake ciki kawai da bai koyawa Banafsha hankali ba, ƙwace kansa yayi ya fice tare da barin gidan gaba-ɗaya, a lokacin ya shige motansa yabar mubi ya nufi Camaroon tun weekend ɗin bata ƙare ba. Abbaa cikin haushi yayi cikin gidan, nan kuma ya tarar da Umaima na aikin kuka, kallonta yayi har yanzu ransa a ɓace ya ce, "Me ya same ki?" Umaima cikin kuka ta nunawa Abbaa hannunta, ta kuma faɗa masa duk abinda ya faru, ƙara tunzura Abbaa yayi, ransa ya kuma ɓaci, lallaɓa Umaima yayi ya shige ɗakin Ummu dan idan yaje wajan Umma yanzu ya tabbata zai yi abinda ba zai yi kyawun gani ko ji ba, amma dai dole ya ɗau mummunan mataki akan Umma da Danish, dole ya take musu birki zuwa yanzu, abu shekaru da shekaru amma kullum cikin stanan yarinya da tsangwamarta, to zai nuna musu iyakar su, yasan abinda zai yi. Ummu stayar da nata hawayen tayi ta ce, "kiyi haƙuri Umaima, in Allah ya yarda haka ba zai ƙara faruwa ba, Abbaanku zai ɗau mataki kin ji?" Ɗagawa Ummu kai kawai nayi ina stagaita kukana, sai da Ummu ta rarrasheni sosai sannan ta ce, "Da banso ɓoye lwa Maminki wannan abinda ya faru ba, amma kiyi haƙuri kada ki faɗa mata kinji, ki bari muji daga bakin Abbaanku, amma dai ba wai ina nufin hanaki zuwa wajan ƙawarki ba kinji, kiyi haƙuri ki rage shiga gidan can, in Allah ya yarda komai zai dai-daita, kada ki faɗawa Maminki dan hankalinta zai tashi sosai, kuma ba za taji daɗi ba, kede ki kiyaye, kada ki ƙara ko haɗa hanya ne da shi." Jinjina kai kawai nayi, tare da share hawayena, Ummu ta fice ta koma gida ni kuma na shige cikin palournmu, cikin rashin sa'a na samu Mamina zaune a palour, kai na a ƙasa na seta muryana na ce, "Sannu da gida Mami" ina gama faɗa nayi ɗakina da sauri. Mami da kallo ta bini, ganin ina ɗingisa ƙafana, ga shi kuma wani ɗankwali na rufe kai na da shi a maimakon taga hijabin makaranta, tun ɗaxu tasan muke dawowa amma taganni shiru, sai abin ya dame ta, tashuwa tayi tabi bayana, amma tana shiga ta samu har na shige banɗaki, daga waje ta ce, "lafiyanki kuwa Banafsha?" Daga cikin banɗakin na ce, "Lafiya lau Mami, wanka nake yi." Mamina ba dan ta yarda ba ta fice kawai, ni kuwa a banɗaki sai da na gama shan kukana, sannan na dirje jikina kaman ba gobe, sai da jikina ya fara zafi sannan na fito, da haushin Ya Danish ya haɗa jikinsa da nawa, sallah nayi na miƙa kukana wajan Allah sannan na yi addu'an musabaƙan gobe Allah bamu sa'a, sai da nayi isha'i sannan na fita, abincin dare na ɗiba na ci ɗan dai-dai, Mami ta sani gaba da tambayan me ya hanani dawowa da wuri? Me ya samu hijabin makarantana? Duk tambayoyin Mamina amsa guda take samu, ba komai ba kuma abinda ya faru, da ta gaji sai ta ƙyale ni ta tambayi batun musabaƙa nan ma na faɗa mata sai gobe za muyi namu in Allah ya yarda, addu'an sa'a ta mini, can ba jimawa na mata sai da safe na shige ɗakina, yau gaba-ɗaya na kasa karatu saboda taƙaici, karshe kawai kwanciya nayi dan nayi bacci ko zan samu nustuwa. Ummu haka ta koma gida ta rarrashi Abbaa da ya bari ya bi abun a sannu, dan Abbaa ya faɗa mata duk abinda Umaima ta faɗa masa, kuma Ummu bata yi musu ba dan tasan staff Umma Sabeera za ta aikata abinda ya fi haka ma, saboda irin stanar da ta yiwa Banafsha mara dalili, Ummu dai wani abu take tunani a ranta amma ta bari ba yanzu za ta bawa Abbaa shawaran ba, yanzu dai ya kwantar da hankalinsa tukunna, sai da ta samarwa mijinta nustuwa, sannan taje wajan Umaima ta rarrasheta ta bata abinci a baki ta bata magani ta shafa mata na shafawa, dan babban yaya sai da ya kai ta chemist kamun ya tafi, ita ma Umaima bata iya karatu cikin wannan daren ba, kwanciya kawai tayi baccin wahala yayi gaba da ita. Yaya babba kuwa ransa yanda yayi mugun ɓaci, ko takan matarsa Hindatu bai bi ba, haka zalika wai ita ma fushi take da shi, an mareta bai yi komai ba sai ma haƙurin da ya bawa Banafsha, ga shi kuma a gabanta ya riƙo hannun Banafsha, kuma ita ko sannu bai ce mata ba, sai ta hau dokin zuciya. Washe-gari Lahadi da wuri su Banafsha suka tafi makaranta, daganan aka wuce wajan musabaƙa, yau da makarantan su Banafsha aka fara, cikin ikon Allah suka yi lafiya suka gama, aka cigaba da sauran makarantun da suka rage, har sai yamma yau ma aka tashi, amma yau kam an kammala sai jiran sakamako. Bayan wani lokaci su Banafsha suka cigaba da zuwa tahfiz, kuma a lokacin hutun boko ya kusa ƙare wa, a haka har sakamakon musabaƙa ya fito, Banafsha ce tazo ta ɗaya, sai Umaima da wata yarinya daga wani makaranta daban suka yi bracket suka zo na biyu, makarantar su Banafsha dai su ne na farko, sai makarantar su ɗaya yarinyan su kuma na biyu, haka dai har wanda suka zo na ƙarshe, kuma an yanke a iya na ɗaya zuwa na biyar ne za'a je na jiha da su nan gaba, dan wannan da aka yi iya na cikin mubi ne, yanzu nan gaba na Adamawa State gaba ɗaya za'a yi kamun kuma aje ga na State da State, wannan nasara ba ƙaramar daɗi ta yiwa malaman su Banafsha ba, kyautar da suka ciyo kuma anbar wa makaranta za'a ƙara gyara abubuwan da ya kamata. Sai da aka kwashe wata guda Ya Danish bai kuma zuwa weekend ba, wanda ganin haka sai Banafsha ta cigaba da shiga gidan, saboda Abbaa da kansa ya bata haƙuri kuma ya ce kada ta yarda ta ce za ta daina shigowa, ita ma gidansu ne kuma shi mahaifinta ne, Umma dai taƙaici kaman ta kashe kanta, duk da girman Umaima kuwa hakan bai hanata jibganta muddin ta gansu da Banafsha, Ummu abun ya isheta dan haka ta yanke hukunci, ta samu Abbaa ta faɗa masa ita dai a shawaranta tana ganin ya auri Mamin Banafsha kawai, Abbaa ba ƙaramin daɗin shawaran Ummu ya ji ba, tunda ita da kanta tayi maganan to yasan ba za ta kawo masa mastala ba, ya amsa shawaran zai auri Mami ko dan Umma ta gyara halinta, dan yasan tabbas ya auri Mami to Umma za ta dawo hayyacinta, sannan ya faɗa mata shi ma zai ƙira Danish ya fito da mata yayi aure, tunda iskanci yake ji, abin nasa tun daga gida zai fara danne yaran mutane, to bai isa ba gwanda yayi aure kamun ya jajuɓo musu abin kunya, nan ma Ummu tayi na'am da wannan hukuncin, ta bisu da addu'an alkairi a cikin lamarin auren daga na Abbaa har na Danish ɗin, amma tare da Farooq za'a haɗasu su fito da matan auren, tunda daman sa'anni ne su ɗin, wannan hukunci Ummu da Abbaa suka yanke, da yake Ummu matar rufin asiri ce kuma mace ce ta gari fatan samun ko wani namiji, shiyasa take ta daban a wajan Abbaa, ita ya aura daga baya, amma baya jin zai iya samun wata kamarta, sosai Abbaa ke ƙaunar Ummu, kuma halayyanta masu kyau ne suke jawo hakan, yana son Umma Sabeera ma, amma dai halayyanta sai a hankali suna ɓata masa rai. Mamina cigaba da rayuwanta tayi, wannan ya zo yau gobe kuma wani daban ya zo, ni har mamaki nake yi ma a ina Mamina ke samo wasu mutanen, gata nan dai ba wai mai yawan fita ba ce, amma kuma jama'a ne da ita kaman mai kasa kanta a tire ta fita da shi, Alhaji Mukhtar kuwa har yau bai zo gidanmu ba, kuma wannan karon ne kawai ya jima, dan wata har da sati guda kenan bai zo ba. Tsakanin yaya babba da matarsa kuwa, mata da miji sai Allah, tuni suka shirya bayan ta gama ginɗaya masa sharuɗan ya fita harkan Banafsha, sannan ta basa haƙuri, shi dai kallonta kawai yake yana murmushin shiririta irin nata, in ba haukan kishi da ya rufe mata ido ba, ai da yana son Banafsha to ba ita zai aura ba, Banafshan zai aura tunda tare ta gansu, kawai ya amsa haƙurin ne ita ma ya bata sun dai-daita, tunda duk sun gaji da fushin da suke yi da juna. Malam Abbo da Banafsha kuwa yanzu stakaninsu ba'a magana, ɗalibai har sun fara ƙus-ƙus ɗin soyayya Malam Abbo ke yi da Banafsha, Umaima ta samu Banafsha ta mata maganam, amma Banafsha ta nuna mata babu komai tsakaninsu, Umaima ma shiru tayi dai tana kallonsu, Banafsha kuwa duk bata kallon abinda ake nufi, ita ta ɗau hakan shaƙuwa ce kawai, yayinda Malam Abbo ke fama da zuciyarsa, kuma zuwa yanzu yana jin ba zai iya haƙura ba, idan bai bayyana mata ba zuciyarsa akwai mastala, shiri yake kawai gadan-gadan na tunkarar Banafsha ya baje mata sirrin ƙalbinsa. Bayan sati biyu muka koma boko inda muka fara sabon aji, semester na farko a ajinmu na ƙarshe, in Allah ya yarda mun kusa gama College of health, ranan juma'a mun je school mun dawo ni da Umaima hankali kwance, mashine ya kawo mu har ƙofan gida, muna sauƙa na hangi motan Ya Danish, nice ma na kula da shi da yake na gane motan nasa, amma Umaima bata kula ba sai hira take mini, ina ganin motan naji haushi ta kama ni amma na kawar, muka yi sallama da Umaima ta wuce gidansu, na shige namu gidan, tun da na hangi mota danƙareriya a cikin gidanmu na ce to Alhaji ya samu zuwa kenan, ajiyan zuciya nayi na shige palourn da sallama, samunsa nayi shi kaɗai zaune a palourn yana waya, stugunnawa nayi na gaishesa ya amsa mini da kai kawai yana murmushi, dan da alama waya mai muhimmanci yake yi, miƙewa nayi na shige ɗakina. Ya Danish da ya kwashe wata guda bai dawo ba, Abbaa ne ya ƙira sa yana buƙatan ganinsa idan bai zo ba zai saɓa masa, shiyasa ma ya zo wannan weekend ɗin, amma ba dan yaso ba, kuma bai haƙura ba shi sai ya koyawa Banafsha hankali. Bayan na wasta ruwa na huta, fitowa nayi dan na samu abinda zan sakawa hanjaye na, da Mamina muka kusa yin karo tana ƙoƙarin shigowa ɗaki na, murmushi ta sakar mini ta ce, "Ai na ɗauka kin zama Amaryan ƙulle ne, abincinma sai na zo na ce ki ci." Cunna baki nayi cikin shagwaɓa na ce, "Uhmn! Ai gani nan na fito Mamina." A gaba Mami ta saka ni har palourn, abincin da ta ɗebo mini ta nuna min na zauna na ci, zama nayi tare da shagwaɓewa na ce, "Mami a bani a baki." Girgiza kai kawai Mamina tayi ta ɗau cokalin ta fara bani a baki, a haka Alhaji da fitowansa kenan daga ɗakinsa ya same mu, wata dakakkiyar haɗaɗɗiyar shadda ya saka yayi mugun kyau, Mamina tun da ya fito ta ke ta binsa da kallo tana murmushi, nima murmushin nayi kai na a ƙasa, Mami ta ce, "Alhaji kyau haka kaman sabon ango." Alhaji Mukhtar hannunsa ya zura cikin aljihun garensa ya ce, "Sabon angon ne ma Insha Allahu, nan ba da jimawa ba, angon Ramlatu." Hararansa Mamina tayi, shi kuma idanuwansa ya mai da kai na, ya ce, "Yarinyata ya kamata yanzu dai ki dinga yi wa Maminki faɗa tunda kin girma, Maminki bata son ta haifa miki ƙanne, ko kema bakya so?" Girgiza kai nayi a hankali na ce, "Ina son ƙanne." Mami hararana tayi, Alhaji kuma murmushi yayi ya ce, "To yanzu dai na yi latti kada na rasa sallahn juma'an nan, bari idan na dawo za mu yi magana, ki labarta mini yanda musabaƙan naku ya tafi." Daga ni har Mami a dawo lafiya kuka masa, sannan ya fice, Mami ta dubeni ta ce, "Faɗima kika ce kina son ƙanne?" Da sauri na ɗaga kai ina murmushi na ce, "Eh Mamina, ki haifa mini ƙani namiji tukunna, sai ki haifa mini mace na dinga mata kisto, kinga nima na samu waɗanda zan dinga yiwa faɗa ina musu wasa, kuma ina cewa ni auntynsu ce." Hararana Mami ta yi ta ce, "Da dai maganan ki haifa mini jikoki haka kikayi da ya fi, amma kibar batun ƙanne, ke kaɗai ma da Allah ya bani alhamdulillahi nagode masa, Allah miki albarka ya nuna mini aurenki, Allah stare mini ke ya stare miki mutuncinki." Wani ɓoyayyen ajiyan zuciya na sauƙe, ina ƙoƙarin kokawa da tunanin da ke son zuwa mini, hamdala nake ta yi a zuciyana ina faɗin, "Ameen." ⭐⭐ CAS Bunayd suna cin abinci amma hankalinsa gaba-ɗaya yana kan waya, General ne yayi gyaran murya ya ce, "My Man za mu ɓata fa." Sosa ƙeya CAS Bunayd yayi ya rufe wayan, a hankali yake cin abinci cikin yanga kaman mace, sai da suka gama ci duka sannan suka tashi suka koma cikin palourn da ke nan a downstairs, babbar budurwan ce ta masto kusa da Bunayd ta ce, "Yaya yaushe za ka tuna promise da ka mana?" Ɗagowa Bunayd yayi idanuwansa akan ƙanwar ta sa mai shekaru 19 ya ce, "Wanne alƙawarin fa Ramlah?" Yarinyar marairaicewa tayi ta ce, "Yaya zuwa Kano fa, ka ce za ka kai mu wajan Majeeder." Bunayd lumshe idanuwansa yayi, sannan ya buɗe su alaman irin ya mance ma da wannan maganan, ba tare da ya kalleta ba ya ce, "banda yanzu sai wani lokacin." Kaman za ta yi kuka ta fara masa magiya, sauran yaran ma mastowa suka yi, suka saka shi a gaba kaman za su yi kuka, duk sun haɗa bakinsu suna cewa, "Please Our Air Force." Gajiya da ihun nasu da yayi a kunnensa ya sanya shi haɗe fuska tare da buga musu wani irin mugun tsawa ya ce, "shut-off!!" Wani irin zabura dukansu suka yi, suka sha nistojin suka koma gefe suka zauna, duk suna muzurai kaman ba su ke masa shagwaɓa yanzu ba, General da ke zaune a gefe yana kallonsu dariya yayi ya ce, "that's My Man, yaran nan duk basa ji gwanda ma ka daina musu dariya." Momsee murmushi ta yi ta ce, "da rabon dai za ka sha kunya Dear.." Bata gama rufe baki ba kuwa, Bunayd ya nunawa yaran gefensa duk suka masto, murmushi ya sakar musu ya ce, "Zan kai ku Insha Allah soon, muna zuwa za mu ɗauko Majeeder ita ma ta dawo nan ɗin, sai ku daina damun mutane da Majeeder-majeeder." Dukkansu murmushi suka yi, ƙaramar ciki mai shekaru 14 ta rungume hannunsa ta ce, "Allah bar mana kai Yayanmu, Allah nuna mana matarka da yaranka." Murmushi yayi ya shafa kanta ya ce, "Ameen Nabeela my love." General kawar da kai yayi tare da haɗe fiska ya ce, "Daman an ce ba'a shiga tsakanin ƴan uwa, to kun fi kusa, ni na daina saka baki ma a harkanku, yanzu nasan maganan Nabeel ma haka za ka biye masa, ko a kanka aka fara yin ƙannene oho, to dai alhamdulillahi nima ina da su Allah ne ya ɗauki abinsa, kuma ƙannen kowa ma za su mutu." CAS Bunayd murmushi yayi tare da miƙewa ya je yayi hugging na General ya ce, "Allah huci zuciyan General namu." Murmushi General ɗin ma yayi ya ce, "Ameen, kuma Allah ya muku albarka, Allah ƙara haɗa kawunanku, yana da kyau kuje Kano ɗin, sannan idan zai yiwu ku taho da mamana Majeeder ɗin, duk ku zo mu zauna ina kallonku hankalina kwance, aikin sojan ma na bar musu." Duka yaran dariya suka saka har Momsee, Bunayd ya juya zai tafi sai ya tuna glass nasa ya bari a palourn sama, kallon yaran yayi ya ce, "Suhaila je sama ki ɗauko mini glass na." Yarinya mai kimanin shekaru 17 ne ta miƙe, da alama ita ce Suhaila ɗin, General kallon Bunayd yayi ya ce, "ka fa gama aikin naka da wuri ka dawo." Murmushi kawai Bunayd yayi ya amshi glass nasa da Suhaila ke miƙa masa, ya ce, "goodnight General namu, Momsee goodnight, my love's goodnight." Duk amsa masa suka yi, ya fice yana murmushi kawai, dan yasan idan ya staya to General zai iya hanasa tafiyan ma gaba-ɗaya, General ma da murmushi ya bi sa da kallo har ya fice, sannan ya sauƙe ajiyan zuciya, kallonsa ya maida kan yaran nasa ya ce, "tunda baku yi wa yayan naku karatunku ya saurara ba, sai ku ɗauko ƙur'ananku ku kawo ni naji, duk wacce bata iya ba kuma tasan sauran." Yaran miƙewa suka yi, kowacce ta ɗauko ƙur'aninta, General na sauraran karatunsu, suka gama ya musu ƙari. CAS Bunayd yana ficewa a palourn ya maida glass nasa, tare da haɗe girar sama da ta ƙasa, hannayensa ya jefa a aljihunsa yana taku cikin ƙasaita, yana fitowa tuni aka buɗe masa ƙofan mota, yana shiga aka kulle suka yi wa mota key, kaman yanda suka zo da mugun gudu haka suka juya da gudun ta da gari, kai sojojin nan basa tausayin kwalta aradu. Maimakon su ɗauki hanyan banana island sai suka ɗau wani hanyan daban, a gaban wani ɗanƙareren gate suka buga horn, suna shigewa suka yi parking, ko da aka buɗe masa ƙofa yanzunma sai da ya ɗau mintuna sannan ya fito, haɗaɗɗen arnen club ne na gani na faɗa, wanda shegun ƙasa kawai ke zuwansa, wajan ya haɗu ya gaji da haɗuwa, tun daga haraban wajan za ka ga kowa da gang nasu, daga masu shanye-shayensu sai masu romance, wasu kuma sex ɗin suke a idon jama'a hankali kwance, mata kuwa gasunan daga masu yawo stirara, sai masu mutunci waɗanda ke saka pant ba bra ko kuma bra da pant. CAS Bunayd tunda ya sauƙa a motan matan wajan ke binsa da kallo, wata ma shafe-shafe suke yi da wani amma ta janye jiki ta tunkaro Bunayd tana girgiza, mata ne suka zagayesa kaman za su yi bandansa kowa na iya juyinta dan ya gani ko zai ƙyasa, amma kaman yanda suka saba kullum hakan ne ta faru, idan mace za ta staya setin idonsa ta buɗe ƙafa to ba zai kalleta ba balle yasan da halittanta a wajan, ko kallonsu baya yi haka ya ci gaba da tafiyansa yana jin waƙansa ta headphone ɗin, sai dai yana ta jan guntun staki kawai saboda haushi, shi gani yake duk basu waye ba tukunna, basu san rayuwa ba, cikin club ɗin ya shiga, classic Bar ya nufa, vip na manya, a wani table ya sama wa kansa wajan zama, ga wani ɗan babban mutun da wata mace suna lashe juna, guntun tsaki ya ja tare ɗan buga table ɗin ya ce, "kabar wannan shashancin ko nayi tafiyana" cikin yarbanci yayi maganan. Babban mutumin wanda da alama Yoruba ne, da sauri ya ture yarinyar gefe ya ce, "Yi haƙuri bansan ka iso ba." Staki Bunayd yaja ya ce, "kana karɓan salihin iskanci ina za ka sani, da nayi magana kuma ka ji, da yake Palace ɗin ya jima da hucewa yayi sanyi, da mai ɗumi kake karɓa ai da ko ihu nayi ba ji na za ka yi ba." Mutumin dai haƙuri ya bawa Bunayd, sannan suka tattauna abinda ya kawo sa, suna gamawa ba ɓata lokaci ya miƙe, sai da ya je wajan rawa ya ɗan taɓa, tunda mata suka fara yanyame sa ya buga musu rashin kirki ya fito yana ta jan staki yana cewa, "aikin banza aikin wofi, za ku tadawa mutum Moransa bayan kunsan Palace naku ya salafce, da masu Palace da ɗumi ake harka ba wanda suka barsa ya gama shan iska ba", haka ya dinga surutu har ya shiga motansa suka nufi gida, yana isa ya wásta ruwa ya haye makeken gadonsa yana juyi, ko da baccin ya gagaresa miƙewa yayi ya ɗaura alwala ya tada nafila kawai. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Duka members na ƳAR KARUWA FAN'S CLUB na gode sosai-sosai da addu'oenku gare ni, jiki da sauƙi sosai alhamdulillahi, ina mai fatan kuma kun mini uzuri na rashin ji na kwana biyu zuwa uku, fan's da ke sauran groups ku ma ina matuƙar Godiya da addu'a, JIKAR IYA fan's, STAR LADY fan's duka da sauran groups da ban ambaci sunansu ba ma ina matuƙar Godiya da addu'a, kuma wannan page naku ne gaba-ɗaya, lurv you all ♥️ اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 46 _ 50 Sai can stakiyan dare sannan Bunayd ya shafa addu'ansa ya kwanta, ba jimawa bacci yayi awun gaba da shi. ** Ni kuwa Banafsha ina son zuwa wajan Umaima, amma na haƙura na kama kai na, dan tunda naga motan ya Danish gabana ya faɗi, yanzu ko hanya banason haɗawa da shi, saboda ni ba zan iya haƙura da faɗa masa magana ba, shi kuma nasan ba zai fasa ci mini mutunci ba. Wankan juma'a muka yi ni da Mamina dukanmu, idan ka kallemu ka ɗauka ba uwa da ƴa bace, kaman yaya da ƙanwa haka muke, muna zaune Mamina na mini photo da wayanta sai ga Alhaji ya dawo, duk sannu da dawowa muka masa, ya amsa tare da miƙo mini ledan staraban juma'a, sai bayan Alhaji ya huta sannan ya ƙira ni, zuwa nayi na zauna cikin ladabi, duk da banson alaƙan Alhaji Mukhtar da Mamina, amma ya zama dole a gareni yin biyayya, dole ne a ce da mijin iya baba, yana kula da ni yana ɗawainiya da ni kaman ƴar cikinsa, kalmansa na ɗazu da ya ce shi angon Mamina ne da yardan Allah sai ya sa stanansa da nake ya ɗan ragu, yanzu ba abinda ya rage mini sai dagewa wajan ganin Mamina ta yarda da maganan auren, tunda na ga alaman ita ce bata so. Alhaji hankalinsa ya mayar kai na ya ce, "Banafsha a bani labarin yanda musabaƙan ta gudana." Kai na a ƙasa na fara zayyanowa Alhaji komai yanda aka yi, da matuƙar farinciki ya ce, "ke ɗin ce dai kika zo ta ɗaya?" Jinjina kai nayi alaman eh, nima fiskana ba yabo ba fallasa, Alhaji kabbara yayi ya ce, "Masha Allah! Lallai kinyi ƙoƙari, kuma abu ya mini daɗi sosai ba kaɗan ba, yanzu dai yaushe kuma za ku yi na cikin Adamawan?" "In Allah ya yarda ba jimawa, duk da dai ba su faɗa mana ba, an dai ce mu dage da karatu, kamun su yayemu ne za'a yi har na State da State duka Insha Allahu" na faɗa kai na a ƙasa. Alhaji murmushi yayi ya ce, "Allah nuna mana da rai da lafiya, amma yaye ku ɗin zai kai shekara ne?" "A'a, watanni ne kawai in Allah ya yarda." "To Masha Allah! Yanzu dai nima akwai nawa kyautan da zan miki bayan na makaranta, amma dai bari mu jira fitowan result naki tukunna, idan shi ma yayi kyau, to sai ki faɗa duk abinda kike so Insha Allah, idan bai fi ƙarfina ba zan miki shi." Murmushi nayi kawai kai na a ƙasa na ce, "Nagode, Allah ƙara girma ya ƙara buɗi." Mamina da murmushi ta shigo palourn ta zauna ta ce, "Banafsha je wajan Ummunku za ta baki saƙo ki kawo mini." Miƙewa nayi na je ɗaki na sako hijabi na, sai na dawo na yiwa su Mami na fice, tunda na fito a gidanmu gabana ke faɗuwa dan bana son ganin ya Danish, sai dai Allah ya taimake ni ban hango motansa a waje ba, har na shiga cikin gidan duka ban ga motansa ba, hamadala nayi na shige da sauri, da Umma na fara yin tozali, tuni na kawar da kai na ban ƙara kallonta ba, dan gani nake idan na ganta ma ya Danish nake kallo, daga nesa na ce, "Umma barka da yamma." Tsaki kawai Umma ta ja, wanda ina da tabbacin har da harara ta haɗo mini da shi, ban staya ƙara yin wani maganan ba na nufi ɗakin Ummu, kuma dai-dai lokacin ta fito, sai da naga Ummu sannan na saki raina na yi murmushi, ita ma Ummu murmushin ta mini ta ce, "ƴar gidan Maminta an shigo ne." Ɗaga kai nayi ina buɗe haƙora na, gaishe da Ummu nayi ta amsa, sannan na ce, "Ummu inji Mamina wai na zo za ki bani saƙo na kai mata." Murmushi Ummu tayi tana miƙo mini saƙon ta ce, "Daga zuwa sai tafiya, yau ko ta kan Umaima ba za'a bi bane?" Ni gaba-ɗaya da yake cikin sauri nake nabar gidan, sai yanzu na tuno da wata Umaima ma, sosa kai nayi na ce, "Ummu bari na dubota, idan na fito sai a bani saƙon", ina gama faɗa na juya na shiga ɗakin su Umaima da sallama. Umaima baccinta take sha hankali kwance, ganin haka kawai na ƙyaleta na fito, ba dan ina sauri banson haɗuwa da ya Danish ba ai da na sola mata dundu na tashe ta, kawai ta ci sa'a ne, faɗawa Ummu nayi tana bacci a bani saƙon kawai na tafi, Ummu ta bani na amsa na musu sai anjima na fice. Bayan fitan Banafsha a palourn sai Mami ta tashi a inda take zaune ta dawo kujeran da Alhaji ke zaune, kallonta Alhaji yayi yana murmushinsa ya ce, "Amaryata ya aka yi?" Tura baki Mami tayi da shagwaɓa ta ce, "kaga banaso Alhaji, haka kawai za ka ɓata mini rai, ni bansan ma me yasa nake sonka har haka na kasa rabuwa da kai ba, kuma kullun cikin ɓata mini rai kake yi, yanzu ko so na ka daina kullum faɗa kake nema da ni", ta faɗa tana juyawa wai tayi fushi. Murmushi Alhaji yayi ya ce, "Allah ne ya ɗaura miki soyayyata kaman yanda nima ya ɗaura mini ƙaunarki da sonki, kuma in Allah ya yarda zan mallakeki, nidai yanzu roƙo na ɗaya ki faɗa mini abu game da danginki, kinƙi bani labarinki kuma kinƙi aminta da aurena, meyasa kike mini haka Ramla? Ina sonki da yawa fa ki taimakeni ki amince da auren nan dan Allah, kar Banafsha ta samu miji a ce za'a yi bikinta kina zaman kanki, sam-sam abin bai yi tsari ba, dan Allah ki amince da maganan auren nan Ramla, wallahi ni kaɗai nasan halin da nake ciki na rashin mallakanki, ni ba zan iya ci-gaba da saɓa wa Allah ba balle na kai ga aikata babban zunubi, ita zina bashi ce kayi da mahaifiyar wani sai anyi da taka, ka yi da ƴqar wani sai anyi da taka, kayi da matar wani sai anyi da taka, kayi da ƙanwar wani sai an yi da taka, ni kuma ko ɗaya bana addu'an haka, dan Allah Ramla ki amince mini muyi komai akan Sunna." Mami ɓata fiska tayi ko kallon Alhaji taƙi yi, Alhaji kaman zai yi kuka ya kamo hannun Mami amma ta ƙwace, riƙo hannunta ya kuma yi ya ce, "Please Ramla say something, dan Allah ki ce kin amince, ko mutum daya a danginki sai mu nema a mana aurenmu, idan bakya so ma sai a ɗaura mana haka al'umman Annabi su zama shaidu da waliyai, dan Allah Ramla, wallahi na miki alƙawarin zamowa uba nagari abin alfahari ga yarinyarki da ma sauran da za ki haifa mini, na miki alƙawarin zamowa miji na gari jajirtacce gare ki, wanda zai tsaya miki a komai ya kuma kula da duk abinda ya shafe ki, sam-sam kada kiji da matata kiyi tunanin ina da mata, banda zafi kam, amma na isa da gidana, dan Allah ki ce kin amince." Zuwa yanzu Mami ji take kaman ta kwaɗawa Alhaji mari, sai ƙoƙarin kwace hannunta take yi, ƙarshe Alhaji kawai sai ya rungumeta ƙam a ƙirjinsa, a take suka sauƙe wani nauyayyen ajiyan zuciya kaman waɗanda suka yi kokawa ko kuma suka yi gudu, Mami lafewa tayi a jikin Alhaji, ba zato ba tsammani yaji hawayenta na ɗiga a kan hannunsa, Alhaji hankalinsa a tashe ya dubeta cikin damuwa ya ce, "Ramla akan aure kike kuka? Dan na ce ki amince ki aure ni? Shikkenan kiyi haƙuri Allah huci zuciyanki, dama kullum idan nayi magana a faɗa muke ƙare wa hakan baya damuna، to faɗa da sauƙi akan hawayenki, hawayenki masu stada ne a gare ni ba zan jure zubansu ba, idan wani yayi sila ma sai inda ƙarfina ya ƙare balle a ce ni da kai na, Allah ya baki haƙuri, in Allah ya yarda daga yau na daina miki maganan aure, in Allah ya ƙaddara hakan, to Allah fahimtar da ke da kansa ya tabbatar mana da alkairi, inkuma babu hakan a ƙaddaranmu shi ma Allah zaɓa mana abinda ya fi alkairi, Allah bamu ikon tuba kamun mutuwa, Allah sa mu gama da duniya lafiya muna amintattun bayi salihai", Alhaji na gama magana ya miƙe ya ɗau key na motansa ya fice. Mami zama tayi a wajan tana risgan kukanta kaman wacce aka aiko wa saƙon mutuwa, a haka har Banafsha ta shigo ta sameta tana kukan, bata ma ji shigowanta ba sai ji tayi muryanta na rawa tana faɗin, "Mamina me ya sameki? Me ya faru?" Haka na ƙarishe maganan nima cikin tashin hankali ganin Mamina na kuka." Mami ƙoƙari tayi ta stayar da kukan ta ce, "Bakomai Banafsha, ki ɗaura mana abincin dare", tana gama faɗa ta miƙe ta amshi saƙonta ta shige ɗakinta, ni kuma guntun ƙwallan da ya zubo mini na share ina addu'an Allah ya yayewa Mamina damuwan da ke damunta, haka na miƙe na yi sallahn la'asar, sannan na shige kitchen na ɗaura mana tuwon dare, duk da ina cikin damuwan abinda ke damun Mamina, amma na tsaya nayi aiki mai kyau, na yi girki na gama, na share palourn har stakar gidanmu tass, na gyara har ɗakin Alhaji ko ina na gidan ya ɗau kyalli, na kunna turaren wuta ko ta ina, ɗakin Mamina na shiga da sallama, sai lokacin na samu tana nata sallahn, banɗakinta na fara wankewa sannan na share ɗakin na kunna turaren wuta, har na fice tana jan carbi, ɗakina na koma na gyara abuna, sai da na gama na shiga wanka na ɗaura alwala tunda Magrib ya kusa, dogon rigana ƴar kanti na saka ta shan iska, zama nayi ina jan carbi har sai da aka yi sallah nayi nima sannan na shafa addu'a na fice. Palourn namu shiru har lokacin Mamina bata dawo ba, Alhaji kuma da naji shiru ni na ɗauka ya tafi ma, sai na je ɗakin Mamina da sallama na shiga, samunta nayi yanzu ma akan sallaya, jikina a sanyaye na ƙarisa gabanta na durƙusa na ce, "Mami abincin na gama." Ba tare da Mamina ta kalleni ba ta ce, "ki ɗiba naki ki ci, sai zuwa anjima zan ci, ki sakawa Alhaji a kula." Amsawa nayi na fice a ɗakin, yanda Mami ta ce haka nayi, amma ni ban ɗiba ba, ina dai jiran Mamina muci tare. Alhaji kuwa yana ficewa a gidan ya je hotel ya kama ɗaki, a can har yayi sallahn Magrib da isha'i, har wajan ƙarfe tara yana can, gaba-ɗaya damuwa ta cika shi, lamarin Mami ya fara basa storo, niya yayi ya koma cikin Yola a daren zuwa gobe ya wuce Kano, amma ya kasa baya jin zai iya tafiya bai sanya Ramlatunsa a ido ba, kwana a hotel ɗin ma ba zai iya ba, haka ya tattara wajan ƙarfe goma ya dawo, lokacin kuma dagani har Mamina babu wanda ya saka wani abu a cikinsa, Mami ko fitowa bata yi ba, ni kuma na kasa cin abincin ni kaɗai, sai da Alhaji ya shigo sannan lokacin naji mostin Mamina, har ɗakina ta shigo ta ƙirani muka je muka ci abincin, Alhaji dai taɓawa kawai yayi dan kar masoyiyarsa taji babu daɗi. Har muka gama cin abinci na musu sai da safe ba wanda ya yiwa wani magana a cikinsu, nidai ina shigewa ɗakina na gabatar da abubuwan da suka kamata, sannan nabi lafiyan gadona na kwanta. Alhaji ma stame hannunsa yayi ya tashi ya shige ɗakinsa, Mami cikin damuwa ta tattare komai, sannan ta nufi ɗakin Alhaji, lokacin shi kuma ya fito wanka kenan, murmushi Alhaji ya sakar mata ya ce, "Masoyiya je ki wásta ruwa kema ina zuwa." Mami jiki a sanyaye ta buɗe baki ta ce, "Alhaji ka yi haƙuri idan na ɓata maka rai.." Dakatar da ita Alhaji yayi yana murmushi ya ce, "kije ki wásta ruwa ina zuwa, kar ki damu kanki ba komai." Ba musu Mami ta juya, ɗakinta ta koma ta shige wanka kaman yanda Alhaji ya ce, Alhaji Mukhtar kuwa murmushinsa yake yi har ta fice, sannan ya shirya, ƙira ne ya shigo wayansa, yana murmushi ya ɗauka tare da amsa sallaman da aka masa a wayan, cewa yayi, "Allah taimaki General." General a nasa ɓangaren murmushi yayi ya ce، "Yaya anwuni lafiya ya fama da jama'a?" "Alhamdulillahi General, ya yaran ya kuma ɗan ka mara jin magana?." General ɗan dariya yayi ya ce, "yaya wani rashin ji my Man yayi kuma?" "Au kana tambaya ne? Tun wuri dai ka faɗa masa yabar ƙirana da Sir idan ba haka ba zan saɓa masa, tunda ya renaka yana faɗa maka General kana amsawa to nidai zan saɓa masa ne, yara ne duk sun mayar da mutane kaman sa'o'insu." "Ayi haƙuri yaya." "Haƙurin dama za ka bayar ai na sani, wannan yaron da macece na tabbata kana aurar da shi za'a dawo maka da ɗan ka, duk la bi ka sakalta shi ka shagwaɓa shi, Allah ya so ma Sojan sama ya ke, da na ƙasa ne kam ai nasan ba iyawa zai yi ba, yanzu ma tausayin matar da za ta zauna da Bunayd nake yi." Dariya General yayi ya ce, "Amma dai yaya ba abinda za mu ce sai godiya, ai in akwai abinda ya fi aikin soja staff my Man zai iya, kuma ai sojojin sama sun fi na ƙasa baiwa, saboda ikon Allah kawai ke sa mutum yana sama kuma ya iya yin yaƙi, sannan duk macen da ta samu Bunayd to ina mai tayata murna ta samu miji nagari." Girgiza kai Alhaji yayi ya ce, "shi yaron naka ne miji na gari a haka? Allah dai ya haɗa sa da wacce za ta iya da shi." General dariya ya kuma yi ya ce, "Nikam ka tuna mini magananmu da shi ranan ma, ya ce na faɗa maka ka nema masa mata wacce za ta dace da shi, ya yarda zai yi auren, kasan yaron nawa da biyayya yake, ga jin magana." Taɓe baki Alhaji yayi ya ce, "Ni ba zan nemawa Bunayd mata ba ya zo ya sa naji kunya, kai dai da kake ubansa sai ka nema masa, koma mene stakaninku ni nawa kallo, yadai tabbatar ya samu matar dan na gaji da kallonsa haka, mutum na neman kai shekaru arba'in amma ya kasa ajiye mata." Cikin raha da ɗan faɗa-faɗa Alhaji yayi waya da General har suka yi sallama kaman kada su kashe, General ma ya sanar da Alhaji za su shigo duka da yaran Insha Allah ba jimawa, Alhaji ya ce Allah ya kawo su lafiya, bayan sun yi sallama sai Alhaji ya miƙe dan tafiya ga masoyiyarsa, yana buɗe ƙofa zai fita ita kuma ta sako kai za ta shigo har kusan karo suka yi, kallonta yayi yana murmushi ya ce, "Na ɓata lokaci ko Hajiyata?" Mami jinjina kai kawai tayi ta juya, ɗakin Mami suka shiga, Alhaji ya samu waje ya zauna, ta zauna gefensa, dukkansu shiru suka yi, sai Alhaji ne ya gaji da shirun ya ce, "Allah ya baki haƙuri, Allah ya huci zuciyanki Ramlatu." Ajiyan zuciya Mami ta sauƙe ta ce, "Kai ma Allah ya huci zuciyanka Alhaji, in Allah ya yarda ba jimawa zan sanar da kai komai a kai na, ka yi haƙuri." Murmushi yayi ya ce, "Bakomai Ramla, yauwa inason faɗa miki daman, bayan kyautan da zan wa Banafsha idan Allah ya sa result nata yayi kyau, to yanzu ina son kiyi haƙuri ki barta ta riƙe waya." Mami ba tare da ta ɗaura idonta akan Alhaji ba ta ce, "a'a Alhaji ba yanzu ba tukunna." "Meyasa ba yanzu ba Ramla?" Faɗin Alhaji yana kallon Mami. Mami ta ce, "Alhaji har yanzu Banafsha yarinya ce, bana son waya ya zama sanadiyyar lalacewan tarbiyan ta, nafi son idan ta samu miji to Masha Allah! Idan ya aureta sai ya saya mata, nan ba mastala matarsa ce, amma ni yanzu storon yarinya ta riƙe waya nake yi." Murmushi Alhaji yayi ya ce, "Eh to wani gefen da gaskiyanki, wani ɓangaren kuma ba gaskiya a magananki, domin komai da kike gani a rayuwa yana da ɓangare mai kyau da kuma ɓangare mara kyau, tabbas a wannan zamani da muke ciki, ƙaramin abu ne yarinyarka a ɓata mata tarbiya ta waya, musamman ƙawayen banza da fasiƙancin neman jinsi yayi yawa, ko kuwa ɓata garin samari, amma fa ina son ki sani, wani a wayan nan zai iya shuka abin alkairin da zai kai sa aljanna, sannan wani a babu wayan ma yana iya lalacewa, addu'a ita ce ke stare komai ta kare kowa, Banafsha yanzu ba yarinya ba ce, ko saboda abinda ya shafi makaranta yana da kyau ki barta ta riƙe waya, yanzu suna final year nasu ne, to wani abun tana buƙatan waya." Mami shiru tayi bata ce komai ba, ganin haka kuma Alhaji yasan me take nufi na bata yarda ba, sai kawai ya ƙyale maganan, nan suka kama hiransu kaman ba abinda ya haɗa su ɗazu har Mami ta fara gyangyaɗi, Alhaji ya ce su kwanta, ba jimawa Mami tayi bacci shi kuma Alhaji a sulale ya tashi ya fice a ɗakin. Washe-gari da wuri Banafsha ta tashi sakamakon ranan asabar ne akwai zuwa tahfiz dan ba su da lecture ba za su shiga makaranta da wuri ba. Banafsha na fitowa gida sai ga Umaima na ƙoƙarin shigowa nasu gidan, murmushi suka sakarwa juna, Umaima ta ce, "Masoyiya muyi sauri lokaci ya ƙure kada muyi latti." "Aikam muka yi latti akwai mastala, yau ba shiga aji kenan sai dai mu dawo mu wuce College dan ba mai taɓa mini lafiyar jikina" na faɗa tare da riƙe hannun Umaima muna tafiya, muna hiranmu a haka har muka isa, Allah ya taimake mu ba'a fara tare lattin ba. Mun yi karatun ranan mun gama har aka tashemu, mun fito muna tafiya ta hanyar da muke bi ta cikin anguwa, sai gani muka yi mutun ya tsaya stegege a gabanmu, ganin wanene dukkanmu sai muka haɗa fiska, Umaima ce ta buɗe baki tana hararansa ta ce, "Malam me damuwanka da mu? Yau kuma da me ka zo?" Garba kallon sama da ƙasa ya yiwa Umaima ya ce, "ke mastalana da ke shishshigi ya miki yawa, ina ruwanki? Ko na miki magana? Na taɓa ƙiran sunanki? Dan Allah ki ƙyaleni nayi da wacce take gabana." A zuciye Umaima ta buɗe baki za tayi magana amma sai na dakatar da ita, kallon uku saura kwata na wásta masa sannan na riƙe hannun Umaima muka wuce, amma still Garba ya ƙara stayawa a gabanmu, a hasale na ce, "ka ɓace mana a hanya." Murmushi Garba yayi yana shafa suɗaɗɗen kansa da yaji askin tanƙwal ya ce, "stakani da Allah na kasa nistuwa, wallahi soyayyanki ta mini mugun kamu, ni ba ruwana da sana'ar babarki, dan Allah ki so ni, kiyi haƙuri da abinda na miki ranan." Hararansa nayi kawai naja Umaima muka wuce abinmu, duk magiyan Garba ko ta kansa ba mu bi ba. Muna komawa kuma muka shirya shirin tafiya makaranta, Alhaji ne ya kai mu bayan ya gama jinjina mana na ƙoƙarin da muka yi, ya ce da Umaima ma ta dage nan gaba kada ta yi bracket, mudai cewa muka yi mun gode, yana sauƙe mu muka shige school, class da muke da shi sai wajan ƙarfe sha biyu, mun yi kuma, mu ne bamu bar makarantan ba sai wajan ƙarfe uku na yamma, muna dawowa Umaima ta shige gidansu na shige namu. Mami da Alhaji na samu suna zaune suna hiransu da fara'a, gaishesu nayi sannan na shige ɗakina, wanka nayi tare da yin sallah, duk da yau ina jin wani yanayi hakan nan, marana ya fara ciwo-ciwo ga ƙafana ya fara kama mini, haka dai a daddafe nayi ayyukan da zan yi ma gida na shirya zuwa tahfiz na yamma, da Umaima muka tafi, yau bayan antashi Malam Abbo ya faɗa mini anjuma zai zo wajena akwai maganan da yake so muyi, nidai nasan ban aikata wani laifin ba, amma na amsa masa sai ya zo, muna komawa gida na samu Alhaji da Mamina za su fita, nima ta ce na shirya muje wanke kai, na ce a'a ni sai gobe, a dawo lafiya na musu, kallo na kunna kawai na kwanta amma inajin ciwon maran nawa na ƙaruwa. Abbaa tunda Ya Danish ya zo jiya ba su zauna ba, sai yau ya faɗa masa da dare yana son magana da su shi da Ya Farooq, duk amsawa suka yi, dare nayi bayan sun yi sallahn isha'i suka amsa kiran Abbaa, a palournsa da ke cikin compound ɗin gidan suka zauna, ga Umma ga Ummu gasunan su ma, Abba gyaran murya yayi tare da mayar da kallonsa kan Umma ya ce, "Sabeera da ke zan fara, saboda kece babba kuma mahaifiya, duk turban da kika nunawa na ƙasa da ke, musamman yaranki to shi za su bi, duk da bansan me yarinyar nan Banafsha da mahaifiyarta suka tsare miki ba, amma na sha faɗa miki ki gyara halayyanki akan su, inason ki faɗa mini me mastalarki da su, dan duk abinda kuka yi ranan da matar kabeeru ya dawo kunnena." Umma Sabeera ɓata fiska tayi ta ce, "Ni ba abinda suka stare mini, halayyan mahaifiyarta ne kawai bana so, kuma ta dena shiga stabgan yarinyata kada ta lalata mini tarbiyaanta, gida kuma ka ce naka ne, dan haka ta shigo banda mastala." Jinjina kai Abbaa yayi ya ce, "Hakan yayi kyau tunda kinsan gida nawa ne, kuma sai wanda na bawa ikon shigowa zai shigo, dan haka kuma ina son ki sani ita Umaima ma yarinyata ce dan haka ni mastayina na mahaifinta na bata daman kula Banafsha da shiga gidansu, in kuma kin ce a'a sai ki nema mata wani uban bayan ni, lalacewa kuma idan Allah ya rubuto mata a ƙaddaranta to ko a ɗakin ki take akan gadonki to sai ta lalace, sannan akan abinda kuka yi ranan zan ɗau mataki ba shiru nayi da na ƙyale ba" Abbaa ya faɗa ransa a ɓace. Umma dai fiskan nan a haɗe, Ummu kuwa kanta na ƙasa ma, Abbaa kallonsa ya kuma mayar wa kan yaransa ya ce, "Ku ma na dawo kanku, musamman kai Danish, kasan abinda ka aikata ba sai na faɗa ba, inason ka sani kai baka isa ka sani jin kunya ba, ni kuma ban haifi mara mutunci a cikina ba da yardan Allah, idan ka ƙara kuskuren aikata irin wannan abun ba iya ga Banafsha ba, wallahi ko a can wajan aikinka naji labari to ka tabbata zan cireka a cikin yarana, ka ji wallahi na ranste maka, bana son hauka da rashin hankali, ina ruwanku da rayuwar su? Haka Allah ya iyo su kuma haka Allah ya so ganinsu, kowa da ƙaddaransa da kuma jarabawansa, su wannan ne jarabawansu, ku zo a banza kuna uzzurawa kanku akan rayuwan mutanen da ba ruwansu da ku, kuma wataƙila a wajan Allah sun fi ku mastayi da komai, ni ba wanda ya bani mamaki sai kai Danish, da iliminka da tunaninka da tarbiyyanka da hankalinka, a bari ita mahaifiyarka da matar wanka su mata ne, kuma mata daman tunaninsu sai a hankali, amma kai za ka haɗa lissafinka da nasu kana na miji wanda ya isa ajiye iyali, to idan ka kuma gigin aikata irin wannan kuskuren ranka zai yi mugun ɓaci, yarinya da tarbiyyanta da komai ta fi wani wanda ya ke ɗan babban Malami nustuwa da komai amma kana neman aikata mata ba dai-dai ba, to wallahi kana ji na ka kiyaye, kuma daga kai har ɗan uwanka ina mai umurtanku da ku fito da matan aurenku akan lokaci dan ba zan ɗau wannan shirmen ba, tun kamun ku fara lalata yaran mutane gwanda na muku aure ku ɗin ma tunda duk kun kai riƙe iyali har kun kai zama iyaye ma, abinda ya sa nayi ƙiranku kenan, kuma duk wanda ya ɓata lokaci zai ga matakin da zan ɗauka, fatan kuna ji na Danish da Farooq?" Dukkansu ɗaga kai suka yi alaman sun amsa, sannan Abbaa ya ƙara musu faɗa sosai ya ce ya sallamesu, su tashi su basa waje, miƙewa suka yi suka fice, Danish fiskansa a haɗe, Farooq dai murmushi yake yi. Bayan fitan su Danish Abbaa ya kalli Umma ya ce, "Sabeera na ƙara dawowa kan ki, ki sani kema abinda kika aikata zan ɗau mataki a kansa ba wai na yi shiru ba ne, matar dai da kika bi kika gallazawa kanki akan ta kuma bata san kina yi ba, to ina so ki sani ita zan auro, wataƙila idan na aureta to za ki dawo hanya ki koma hayyacinki, yarinyar ma nan za ta dawo da zama, kuma kika kuskura kika ce za ki aikata wani rashin hankalin to zan nuna miki abinda ke kai na ya fi naki, ai mutum ba shi yake yin kansa ba, dan mahaifiyarta na zaman kanta, ai ba yana nufin a staneta a stangwameta ba, ko akwai wanda yake zaɓawa kansa daga cikin iyayen da zai fito? Kowa da kike gani Allah ne ya riga ya gama stara komai a kansa tun fil'azal, dan haka ki dawo hayyacinki, bai kamata ke da za ki yiwa wasu faɗa, a ce ke da kanki kike aikata hakan ba, idan kuka tsamgwami yarinya kuka dinga kyamatarta, wani hali kuke tunanin za ta faɗa? Ai sai ta zaɓi ita ma ta shiga duniya tunda haka al'umma ke mata kallo, duk irin munin halin mutum, maganin zama da shi ake sha, sannan a ja shi a jiki a dinga nusar da shi gaskiya ana nuna masa abinda ya kamata, amma idan aka dinga ƙuntata masa to gaba-ɗaya ba za'a ribatu da mutum ba, yanzu idan yarinyar nan ta lalace kuma wani a yaranki ya bi ta shi ma ya lalace ya za ki ji? Kuma wa gari ta waya? Amma idan ta shiryu bata lalace ba ai ko ke hankalinki a kwance kinsan yaranki ba za su bita da ɓatanci ba idan ba maganan arziƙi ba, ba'a kyamar mutum ko ƙuntata masa ko da kafiri ne balle kuma musulmi wanda ya ke salla kai ma kake sallah, ya ambaci Allah da Manzonsa kai ma ka ambaci Allah da Manzonsa, akwai wani kissa na wani sahabin Manzon Allah SAW da ya kwanta mini, amma dai shi ma akwai wani abu da yake yi wanda ya zamana mutane na ƙyamatan shi, amma Annabi ya nusar da su hakan ba kyau ya ja bawan Allahn a jiki, daga ƙarshe sai da ya zama sahabi mayaƙin Annabi SAW wanda ake ji da shi, to ba'a rena ɗan Adam duk yanda ya je kuma ba'a ƙuntata masa, misalai dai da yawa akwai su kuma Annabi da kansa yayi magana akan hakan, dan Allah dan Annabi ki kiyaye Sabeera, wannan yarinya tamkar Umaima haka take a wajanki, Ummu-khultum ke ma abinda ya sa na ajiye ku, duk so nake ku gyara, mu gudu tare mu stira tare, duk da bantaɓa jin kin yi musu wani abun da ba dai-dai ba amma a kiyaye saboda zuciya watarana sai a hankali, kuma ku yi haƙuri amma zan ƙara aure, Insha Allahu dai ita Maman Banafsha zan aura, fatan za ku bani haɗin kai kuma ku ci gaba da tayani da addu'an alkairi." Ummu tana murmushi ta ce, "Allah taimaka ya kuma tabbatar da alkairi, Allah shige mana gaba ya sa mu fi ƙarfin zuƙatanmu, Allah kuma ya baka ikon yin adalci." Murmushi Abbaa yayi ya amsa da Ameen, sannan ya dubi Umma ya ce, "Sabeera ke kuma ba ki da abin cewa ne?" Umma cikin fushi ta miƙe fuuuu! zuciyanta na tafarfasa kaman za ta kifu akan Abbaa ta ce, "yanzu dan ka gama rena mana hankali ka rasa wa za ka auro sai gantalalliyar karuwa da ta gama yawon karuwancinta, wa ma ya sani ko tana ɗauke da ciwo, ka zo ka aurota ka raɓa mana, to wallahi ba da ni ba, kuma ban yarda ba ban amince ba, idan ma auren za ka yi jaraba na damunka ba ka godewa Allah da mata biyun ba, to sai dai ka auro wata amma banda wannan wastatstsiyar" tana gama faɗa ta fice. Abbaa murmushi kawai yayi ya sallami Ummu, ya kwanta abinsa ba damuwan komai a zuciyansa, ransa wasai, sai addu'an fatan alkairi da yake yi, da kuma Allah haɗa yaransa da mata nagari. Ya Farooq farinciki yake abinsa bai da damuwan komai, daman budurwansa ta faɗa masa an ce ya turo, yana niyan yiwa Abbaa magana kenan ya musu wannan magana, shi dai ya Danish cin rai kawai yake yi, shi yana da budurwan amma gaskiya ya rasa dalili tunda incident ɗin nan ya faru stakaninsa da Banafsha, sai ya fara jin haushin budurwansa haka kawai, ga shi tunda ya zo weekend ɗin nan, gobe Sunday zai koma amma ko kallonta bai yi ba balle ya mata wani mugunta, dan shi bai huce ba har yanzu, Ya Farooq na masa magana ma amma ko kula shi bai yi ba, kuma bai shiga cikin gida ba dan baya son surutun Umma. Ina kwance na gaji da kwanciya na miƙe nayi ayyukan da ya kamata, wanka na shiga na gama na shirya, ina zaune shiru ni ɗaya a gida har nayi sallahn Magrib su Mamina ba su dawo ba storo ma ya bi ya cika ni, kaman nayi kuka haka nake ji, ga shi banda waya balle na ƙira Mamina, da ace ba weekend bane sai na shiga gidan su Umaima, amma weekend ne bana buƙatan haɗuwa da Ya Danish dan nasan yanzu haka ba zai wuce ma suna ƙofan gida ba, haka na daure na zauna cikin storo. Malam Abbo sai da ya shirya zuwa wajan Banafsha abincin ruhinsa, sannan ya bi masallaci yayi sallahn Magrib, ana idarwa ya tashi ya kamo hanya cike da addu'an Allah bashi ikon furta mata soyayyansa, kuma Allah ya sa ta amsa, dan sosai take masa kwarjini, Malam Abbo ba ƙaramin kwalliya ya ci ba, ga wani ƙamshi da yake yi na musamman, Malam Abbo haɗaɗɗen matashin saurayi ne wanda ba macen da sa ta kallesa bata ji ya burgeta ba, cikin tafiyarsa na nistuwa yake taku har ya iso ƙofan gidan su Banafsha, kuma ya wuce su ya Danish a ƙofan gidansu, ya Danish kallo ɗaya ya masa ya ganesa, shi ne saurayin da yake ganinsu tare da Banafsha, tuni wani haushi ya rufesa da ya tuna abubuwan da ta ke masa, ga shi ranan bai samu ya koya mata hankali ba, ƙwafa yayi ya bi Malam Abbo da harara. Dai-dai isowan Malam Abbo ƙofan gidan su Banafsha, dai-dai isowan motan Alhaji sun dawo daga anguwa da Mami, Alhaji da kansa ya sauƙa ya buɗe gate ya shige cikin gidan, Mami da yake ta kalli Malam Abbo, sai ta faɗawa Alhaji ai malamin su Banafsha ne ya masa iso, ta juya ta shige ciki shi kuma Alhaji ya fice waje, Malam Abbo yana ganinsa ya fara fara'a, cikin mutuntawa suka yi musabaha suka gaisa, sannan Alhaji ya masa iso suka shige cikin gidan. Mami na shiga ta sameni zaune sturu-sturu da idanuwa kaman an tare kule a buta, duk a storace nake, murmushi tayi ta ce, "Sannu da gida ƴar Mami mai storo." Ina murmushi na tashi na rungume Mamina na ce, "sannunku da dawowa Mamina." "Yauwa Faɗiman Mami, ki shige ki sako hijabi dan naga malaminku ya zo" Mami ta faɗa tana nufan ɗakinta. Ajiyan zuciya na sauƙe dan storo ya tafi tunda Mami ta dawo, ɗakina na wuce ina murmushi dan sai yanzu da Mami tayi magana sai na tuna Malam Abbo ya ce zai zo gidanmu, amma mamaki nake da zuwan da yayi da dare da kuma ko me ya kawo sa Allahu a'a lamun, nidai ya ce akwai maganan da za mu yi, addu'a nake Allah ya sa alkairi ne, kuma Allah yasa ba wani laifin na aikata ba. Alhaji tare da Malam Abbo suka shigo palournmu, waje Malam Abbo ya samu ya zauna, Alhaji ya shige ɗakin Mamina ya faɗa mata malaminnamu ya shigo, Mami ta amsa shi kuma ya wuce ɗakinsa, Mami cikin kamala ta fito da hijabinta, Malam Abbo kuwa cikin ladabi ya durƙusa ya gaidata yana ya sunne kai, Mami amsawa tayi da fara'a bata ce komai ba ta dai ce bari ta ƙira masa faɗima, ya amsa yana mai sunkuyar da kai cikin kunya. Ni kuwa ina shiga ɗakina haka kawai na stinci kai na da ɗan gyara fiska na, na shafa humrana sannan na ɗau hijabina na saka, ba ƙaramin kyau nayi ba ga shi har da man baki da kwalli na saka, Mamina ce ta shigo ɗakin da sallama, kallona tayi ta girgiza kai ganin har da kwalli na saka, murmushi kawai tayi ta ce, "Idan kin gama kwalliyan to yana jiranki" tana gama faɗa ta fice tana murmushi dan yanzu ta fara harbo jirgin abinda ke shirin faruwa, Banafsha har da kwalliya, shi kuma malamin nata sai sunne kai yake kaman mara gaskiya. Mamina na fita na tsaya na gama dariyana sannan na tattaro nistuwata na fice palourn ina mai jin wani iri haka kawai, ina isa da sallama ya amsa mini, waje na samu na zauna a ƙasa, amma yau Malam Abbo ya dage firr! Sai na zauna a sama, haka ba dan naso ba na zauna a sama ina cusa fiskana a cikin hijabina, da hijabin a bakina na gaishe sa muryana yayi wani iri, shi kuma ya amsa yana kwaikwayon muryan nawa yanda yayi, sai abin ya bani dariya kawai na ɗan murmusa nayi shiru tare da yin ƙasa da kai na, ina wasa da yastuna. Malam Abbo can da shirun yayi yawa sai yayi gyaran murya ya ce, "Malama Faɗima yau ba ruwan sha ne, abin rowa aka fara mini." Kunya na ji na miƙe da sauri, ni gaba-ɗaya na sha'afa ma, wucewa nayi kitchen na haɗa masa abin taɓawa har da tuwon dare da nayi, na ɗauko cikin nistuwa na zo na ajiye masa agabansa, murmushi Malam Abbo yayi ya ce, "ina godiya Malama Faɗima Allah ya yi albarka, sannu da ƙoƙari." Ina sunne kai na amsa da ba komai, sannan na ce, "ka taɓa abincin dai malam, ka ji girkin ɗalibarka." Malam Abbo cikin fara'an yanda na sake ya ce, "Masha Allah! Ai dole na taɓa Sayyadata" ya faɗa tare da kurɓan ruwa, sannan ya dube ni, cikin jarumta ya fara mini magana kaman haka, "Sayyada Faɗimah fatan dai ban takura ki ba da zuwan da nayi na dare?" Jinjina kai nayi kawai alaman ba komai, murmushi Malam Abbo yayi ya ce, "To! Godiya nake Sayyadata, Allah ƙara lafiya." Murmushi nayi kawai, sai da muka gaisa ya tambayi karatu da boko duk na amsa masa, sannan ya ɗago yana bi na da wani irin kallo mai narkar da zuciyan abinda kakeso, ƙasa nayi da kai na, Malam Abbo ya numfasa ya ce, "Sayyadata ina mai fatan babu wanda ya rigani ko ya mini shigan sauri ya mini ƙafa?" Ba tare da na fahimci abinda yake nufi ba kawai na ɗaga kai, murmushi ya kuma yi ya ce, "Masha Allah! Alhamdulillahi ala kulli halin! Ni ɗin mai sa'a ne Insha Allah, Sayyadata abin da nake faɗa da gaske nake faɗansa tun daga ƙasan zuciyata, soyayyanki da ƙaunanki sun jima da yi mini mugun kamu, kuma ƙauna ce wacce aure za ta zama ribarta Insha Allah, ina fatan za'a amsheni hannu bibbiyu tunda an ce babu wanda ya rigani." Wani irin kunya ne ya rufe ni lokaci guda, kawai rufe fiskana nayi da hijabi ina ta murmushi, ba wannan bane karo na farko da namiji ke faɗa mini yana ƙaunata, amma wannan sai na ji sa daban, Malam Abbo ya kai maƙura duk inda ake buƙatar mijin aure ya kai, alhamdulillahi indai wannan ya zamo uba ga yarana to ina da tabbacin sun yi dacen uba, amma sai dai kashh! Ba wannan bane a gabana, ban da asali ban da kowa sai Mamina kawai, aure ba zai yiwu ba a gare ni, ba zan iya yaudaran bawan Allah ba na sa masa rai ba, ni na riga da na sani a ƙaddaran rayuwata babu aure, kowa na zagina da hantara ta akan ƙaddaran mahaifiyata, a yanzu zan iya jurewa amma ba zan iya jure hakan a gidan aure na ba, ko ga dangin miji ko kuma aje-aje har shi mijin da kansa, dole na haƙura da batun soyayya balle a kai ga aure, cikin sanyin jiki na ɗago shanyayyun idanuwana da ke neman zubar da ƙwalla na kalli Malam Abbo cikin ido, da duk sauran juriyata da jarumtata na ce, "ka yi haƙuri Malam, amma ni ba zan yi aure yanzu ba kada na bata maka lokaci." Daga yanayin Banafsha Malam Abbo ya fahimci ya samu karɓuwa, ko abinda take furtawa ma kokawa take da zuciyanta wajan faɗan hakan, cikin damuwa ya ce, "Sayyadata ko nan da shekara nawa ne na miki alƙawarin zan jira ki, nasan ba zai wuce kina son kammala karatunki ba, wallahi banda mastala da bokonki ni da kai na idan ina da hali sai iya inda rai ya stayar da ni akan iliminki, ina ƙaunanki Sayyadata, na jima ina dakon soyayyanki amma na kasa furta miki, wannan karo da na samu ƙwarin guiwan faɗa miki dan Allah kada ki juya mini ƙoƙon barana ba tare da kin cika mini shi ba." Zuwa yanzu hawayena ƙiris suke jira su kwalalo, a hankali na ce, "ka yi haƙuri Malam Abbo ba zan iya aurenka ba." Cikin damuwa yake kallona yanda nake kallonsa ya ce, "Saboda menene Malama Faɗima? Halinane bai miki ba? Ko nasaba na? Ko kuma menene ba dai-dai ba ki faɗa mini, na miki alƙawarin gyarawa yanda kike so in Allah ya yarda." Wannan karon muryana na rawa har hawaye sun fara bin kuncina na ce, "Malam nasan kasan gaskiya akan komai a rayuwata, nasan kasan duk abinda jama'a ke faɗa a kai na da mahaifiyata, Malam ba ta inda ka kasa, don babu macen da za ka nuna kana sonta ta ce baka mata ba, Malam ni kwata-kwata auren ne ba zan yi ba a rayuwata." Malam Abbo kallon Banafsha yake ba kifta ido ya ce, "Zan aureki a haka Faɗima, zan aureki a duk yanda kike, ni ke nake so ba komai da ya shafe ki ba, ko wanni bawa da irin ƙaddaransa da kuma jarabawansa, ina ƙaunanki a duk halin da kike ciki Sayyadata." Fashewa kawai nayi da kuka na ce, "Malam ko kana so na danginka ba za su aminta da ni ba na sani, dan Allah ka yi haƙuri Malam, Allah ya baka mace tagari wacce ta dace da kai", ina gama faɗan haka na miƙe ina kukana na nufi tafiya ɗakina. Malam Abbo ma miƙewa yayi ya fara magana wanda shi ya stayar da ni, "Malama Faɗima kaman yanda na faɗa miki ina sonki a duk yanda kike, to ina son ki sani ke ce dai-dai ni, kuma ni zan zauna da ke ba kowa nawa ba, ina sonki ina ƙaunanki ki saka wannan a ranki, in Allah ya yarda in har da rabo kuma da alkairi to Allah da kansa zai yi Allahnsa ki zama mallakina, amma ina roƙon ba za ki ɗau fushi da ni ba akan wannan magana." Ina gama sauraran Malam Abbo na wuce ɗakina da sauri ina kukana, ga samu ga kuma ráshi lokaci guda, Malam Abbo mijine da ko wacce mace tagari za ta yi addu'an samu, amma ni ga daman hakan ya sameni har gida sai dai babu hali, ƙaddaran mahaifiyata ya riga ya rusa mini komai nawa, ƙaddaran mahaifiyata ya sa na tashi banda kowa sai ita dan ina da tabbacin ƙaddaran rayuwanta ne ya rabata da kowa nata, ƙaddaran amsa sunan ƴar Karuwa da zamtowa ƴar Karuwa shi ne babban ƙalubale na a rayuwa, ɗaga hannayena sama nayi na ce, "Allah ga ni gare ka, Allah ka iya mini a lamurana, a yanda nake ina matuƙar son na ga nima na raya sunnan ma'aiki, amma mahaifiyata ta zama katanga a gareni tsakanina da aure, wa zai auri ƴar mace mara asali kuma ƴar karuwa? Banda Uba banda ƴan uwa banda kowa sai mahaifiya, ai ko a jikin bishiya na fito albarka, nasan babu ubanda zai amince ɗan sa ya auri ƴar mace mai zaman kanta, macen da maza daban-daban ke sintiri a wajanta" rushewa nayi da kuka mai ƙarfi saboda ciwon marana da ya ƙaru ya dawo mini sabo fill dan damuwan da nake ciki. Malam Abbo kuwa Banafsha na shigewa kaman zai yi kuka ya koma ya zauna, sai da ya ƙara kurɓan ruwa ya dinga jera ajiyan zuciya sannan ya miƙe, ya juya zai fice sai ga Alhaji ya fito a ɗakinsa, Malam Abbo daurewa yayi ya shanye damuwarsa da murmushin yaƙe suka ƙara musabaha da Alhaji ya masa sai da safe, sai da ya rakasa har ƙofa sannan suka yi sallama ya tafi, Alhaji kuma ya rufe ƙofa ya dawo cikin gidan cike da tausayin wannan matashin, dan kusan maganansu na ƙarshe da Banafsha ya ɗan stinci saura, wannan jarabawa ce ga uwa da kuma ƴar ta, kuma Alhaji sam-sam bai ga laifin Banafsha ba saboda gaskiyanta ne, wasu iyayen sai a hankali ba lallai su amince ɗan su ya auri mara asali ba kuma ƴar mace, amma kuma yana tausayin saurayin dan ji yayi kaman yaronsa ne ya je neman aure aka masa haka, addu'an alkairi kawai yayi ya tura ƙofan Mami ya shiga, ganin tana bacci sai ya fice ya koma nasa ɗakin ya kwanta. Malam Abbo yana fitowa ya samu har lokacin su Ya Danish na zaune a ƙofan gida, duk da duhun dare amma Ya Danish yana ƙoƙarin hango wani abu daga yanayin Malam Abbo, kaman zai ji daɗi kuma sai ya taɓe baki irin me damuwansa da kashin su, shi kuwa Malam Abbo haka ya koma gida cikin damuwa da niyan zai bawa Banafsha lokaci ko da sati guda ne ya ji ko ta sauya shawara, idan kuma abun ya ƙi to gaskiya zai samu Ummanta da maganan, shi ba zai iya jure rashin Banafsha ba, Allah ya gani soyayyanta ya jima da masa mugun kamu. Ya Danish har suka gama hiransu suka shige gida zuciyansa cike da son ganin giftawan mara kunyar, ya samu ya mata wani rashin kirkin ko zai ji daɗi, haka washegari da sassafe ya fito tun su Umaima ba su tafi makaranta ba ya zauna a ƙofan gida yana son kallon giftawanta dan ya yaɓa mata magana. A ɓangaren Banafsha kuma da wani irin mugun zazzaɓi ta kwana da ciwon mara, kamun gari ya waye tuni ta fice a hayyacinta, daman ita idan ciwon maranta ya tashi ba ya mata ta sauƙi, duk wata na Allah sai ta ji a jikinta, balle kuma ga shi jiya abin ya haɗu mata biyu, ga damuwa ga ciwo, kwata-kwata ko sallahn asuba ta kasa tashi ta yi, ta galabaita sosai-sosai kuma har lokacin ba wai jinin ya zo ba ne. Ko da safiya tayi, Mami jin shirun tayi yawa, sai ta ɗauka ko yau Banafsha rigimanta ne ya mosta, da kanta tayi ayyukanta ta yi wanka chass abinta, Alhaji kam ya koma bacci daman baisan me ake ciki ba, Mami ganin dai har lokacin ba mostin Banafsha kuma lokacin makaranta ya wuce, sai ta nufi ɗakinta tana surutu, tana tura ƙofan ɗakin ta shiga ta samu Banafsha yashe a stakar ɗakin a sume, salati Mami ta rafka dan sai yanzu ta tuno lokacin al'adan Banafsha ya yi, month nata ya zagayo, cikin damuwa ta fice ta ɗauko ruwan zafi, shafa mata a fiska Mami tayi, sannan ta sa mata a baki, ruwan na kai wa maƙoshinta ta sauƙe wani wawan ajiyan zuciya, a hankali ta buɗe idonta da suka rine saboda azaban ciwo, ruwan zafin Mami ta bata ta sha sosai kaman ba mai zafi ba ko cire baki bata yi ba sai da ta shanye tass, sannan ba jimawa ta dinga kwarara amai, sai lokacin ta samu salama dama-dama ta koma ta kwanta, Mami sai aikin jera mata sannu kawai take yi, a haka ta tashi ta gyara wajan aman da ta yi, ta cire mata kayanta suka shige toilet ta gyara mata jikinta, sanin ba lallai in tayi sallahn asuba ba, sai ta mata alwala, suna fitowa ta shiryata staff ta saka mata hijabinta, a haka a zaune ta ce tayi sallahn kamun taje ta taso Alhaji su tafi asibiti, Banafsha amsawa tayi da kai, Mami ta fice. Ya Danish na zaune a ƙofan gida har su Umaima suka fito, yana tunanin ko za su biyawa Banafsha amma sai suka wuce abinsu, Ya Danish bai san idan yana ƙofa Umaima bata biyawa Banafsha ba, haka suka yi tafiyansu da Nana, sun je makaranta ana ta karatu Umaima ta zuba ido ta inda Banafsha za ta ɓullo amma shiru, haka malamai suka shigo har Malam Abbo ma aka musu darrusa har aka tashi ba Banafsha ba alamanta, Umaima duk ta bi ta damu dan tasan idan ba wani abun bane ya faru to Banafsha ba za ta ƙi zuwa makaranta ba. Ɓangaren Malam Abbo ma bai ji daɗi ba dan gani yake shi ya ja mata rashin zuwa makaranta, sai duk abin ya bi ya damesa, ko da aka tashi ya daure dai bai tambayi Umaima ba yana tunanin zuwa yamma Banafsha za ta zo, dan Maminta ba za ta barta ta zauna a gida ba. Ya Danish har ya gaji da zama ya shige gida, har su Umaima suka dawo, shiru ba giftawanta, Umaima ma ko da suka dawo ba ta shiga gidan su Banafsha ba, ta bari sai zuwa yamma dan tana tunanin ko wani abun ne ya kuma faruwa tsakanin Banafsha da mutanen Mami ya sanyata fushi taƙi zuwa, bata son taje dubo Banafshan kuma ta kalleta cikin damuwa, sai tayi zamanta cike da kewan ƙawarta aminiyarta. Mami ɗakin Alhaji ta shiga da damuwa ta tashesa a baccin, faɗa masa abinda ke faruwa ta yi, Alhaji da yake shi ma yasan da ciwon Banafsha, cikin hanzari ya shige banɗaki ya wanke fiska, bai yi kowa wanka ba ya zura jallabiyansa ya fito, Mami ta shiga ta samu Banafsha ta idar da sallahn, kamota tayi suka shige motan Alhaji, shi kuma ya ja sai asibiti, duk da safiya ne amma Allah ya taimakesu da yake asibitin kuɗi ne kuma babban asibiti ne, likita yayi attending nasu an mata alluran da aka saba mata, aka basu magani sannan suka juyo gida, suna dawowa kuma ba jimawa jinin ya zo, nan ma ɗin wani ciwon maran ne dan sai Mami ne ta gyara mata jikinta staff, haka suka wuni cass! Alhaji daman sai Monday zai koma dan haka yana gida, Mami sai kula take da yarinyarta tana mata addu'an Allah ya yaye mata wannan ciwon maran jaraban. Yamma na yi bayan ya Danish ya shirya tafiya ya fito ya staya a waje, nan ma dai shiru har su Umaima suka kuma wucewa yana wajan, saboda ganinsa Umaima bata yi gigin zuwa gidan su Banafsha ba, ya Danish gajiya yayi ganin su Umaima suna dawowa an tashe su ma, sai ya ja guntun tsaki ganin babu ita ya shige motansa yayi tafiyansa ko sauraran abokinsa IB bai yi ba. Umaima kuwa suna zuwa makaranta nan ma babu Banafsha har aka tashi, cikin damuwa dai Malam Abbo ya tambayeta ƙawarta ko lafiya bata zo ba, Umaima ta faɗa masa bata sani ba dan bata dubo ta ba, amma za ta duba ta, amsawa Malam Abbo yayi yana addu'an Allah ya sa lafiya, Umaima suna komawa suka samu sai lokacin ya Danish zai tafi, shigewa gida suka yi, ta ce sai ya tafi da anjima za ta je ta dubo masoyiyarta. Sai da suka yi sallahn Magrib sannan Umaima ta samu Ummu ta ce, "Ummu zan je wajan masoyiya Banafsha, yau kwata-kwata safe da yamma du bata je makaranta ba bansan me ya faru ba." Jinjina kai Ummu tayi cikin damuwa ta ce, "To Allah ya sa dai ba wani abun ba ne ya faru kuma, wannan yarinya Allah bata miji nagari inda za ta huta, Allah dai-daita mata lamuran mahaifiyarta." "Ameen Ummu ba na je, sai na dawo." "To ki dawo lafiya, ki ce ina gaisheta, idan ba komai ki dawo da wuri saboda Abbaa kada yayi faɗa kin fita da Magrib, idan kuma wani abun ne ki kwana can zan faɗa masa, Allah muki albarka dukanku ko" faɗin Ummu. Umaima ta miƙe tare da cewa, "Ameen Ummuna" ta fice a ɗakin, tana ƙoƙarin fita a ƙofan palourn su ta jiyo muryan Umma na faɗin, "Ina za ki je da daren nan bayan anyi Magrib? Abbaanku bai hana ku fita da dare ba?" Umaima tura baki tayi ta ce, "Na faɗawa Ummu fa, kuma wajan Banafsha zan je ni, yau bata je makaranta ba kwata-kwata bansan ko bata da lafiya ba." Wani kallo Umma ta mata ta ce, "Ita wacce kika faɗawa ita ce uwarki ko ubanki? Umaima zan yi mugun saɓa miki fa, wallahi ki fita a idona na kulle, na ce sannu Uwar Banafsha, ke ce karuwa uwar Banafsha ƙarshenta kenan, to maza ki juya ki koma ɗakinki, idan kika fita a gidan nan yau ba wanda ya isa ya hanani karyaki, ba dai kinga Danish ya tafi ba ko? Shi ne za ki stiro da wani hali, kullum na miki magana bakyaji, to ni nan zan karyaki, wuce ki koma kamun na taso" Umma ta ƙarishe maganan da mugun stawan da sai da Umaima ta ɗan firgita, tura baki tayi ta wuce ɗakinta tana kuka an hanata dubo Banafsha, Umma kuwa ƙwafa tayi ta koma ta zauna ta ga ta inda Umaima za ta fita, duk abinda ya faru Ummu ta jiyo amma sai ta yi shiru, ko ba komai ba'a shiga tsakanin uwa da ƴa, da gaskiyanta ita ce mahaifiyarta ta fi ta iko da Umaima, jan baki Ummu tayi ta yi shiru akan zuwa gobe Insha Allahu ita da kanta za ta je ta dubo Banafsha ɗin. Washegari Monday bayan Umaima ta shirya tafiya makaranta kasancewan Monday ne suna da class na safe, sai Umma ta fito, mugun kallo ta bita da shi sannan ta ce, "Umaima kina fita ki wuce makaranta, idan kika kuskura kika bi gidansu yarinyar nan wallahi ranki zai yi mugun ɓaci, bana son shashanci, idan mutuwa ta yi ma ina ruwanki? Ko akwai wanda aka ce ba zai mutu ba ne?" Umaima yanzu ma tura baki tayi haka ta fice, tana kallon gidan su Banafsha tana son zuwa amma tana storon Umma, haka ta wuce ta tafi makaranta, kaman yanda ta yi tsammani kuwa ba ta ga Banafsha a boko ba har suka gama class nasu wajan ƙarfe huɗu ta dawo gida, nan ma dai ba daman zuwa tana storon Umma haka ta shige gida, tana shiga kuwa ta samu Umma a palour, wani kallo Umma ta mata ko amsa gaisuwan da take mata bata yi ba ta ce, "kinje gidan ƙanwar uwartaki ko?" Umaima girgiza kai tayi ta wuce kawai, Umma ta yi ƙwafa ta ce, "Ya fi miki, ai da kinje wallahi sai na kusa karyaki, kuma ki gama abinda za kiyi maza ki fito ki shirya ki tafi tahfiz, kuma kika sake kika bi gidansu sai na miki baki." Umaima haka ta ci abinci ta yi sallah ta wasta ruwa, sannan ta shirya ta wuce islamiyya, yau ma shiru ba Banafsha ba alamanta, Malam Abbo duk ya bi ya damu, ga shi yana son ya bata sato guda tukunna ya kuma komawa, bayan an tashi ya tambayi Umaima lafiya kuwa ko akwai wani abun da ya hana ƙawarta zuwa makaranta, Umaima kaman za ta yi kuka ta ce bata samu zuwa ba, amma Insha Allah anjuma za ta je. Malam Abbo cikin damuwa ya ce, "Allah ya kai mu anjuman, ki faɗa mata ina gaidata, na yi kewanta" yana gama faɗa ya wuce. Umaima da kallo ta bi Malam Abbo, duk mamaki take yanda ya bi ya damu haka shi ma, duk da dai tasan masoyiyarta tana da shiga ran duk wanda ya zauna da ita saboda halinta masu kyau, haka Umaima ta juyo gida ita kaɗai da aka tashi, nan ma Umma ta kuma faɗa mata kada ta kuskura ta ce za ta je gidan su Banafsha, Umaima ko Ummu bata yi wa magana ba taja bakinta tayi shiru, sai da Abbaa ya dawo wajan isha'i sannan ta miƙe saɗaf-saɗaf ta tafi sashinsa, da sallama ta shiga. Abbaa yana murmushi ya amsa mata ya ce, "shigo ko Umaimatun Abbaa." Umaima shiga tayi ta samu waje ta zauna, gaishe da Abbaa tayi ya amsa, ta amsa sannu da dawowa. Abbaa ya ce, "Ya aka yi Ummul-khultum kaman akwai magana a bakinki? Wa ya taɓa mini ke?" Umaima sarkin taɓara, tura baki tayi cikin shagwaɓa ta ce, "Umma ce Abbaa." Murmushi Abbaa yayi ya girgiza kai dan yasan za'a rina, yana kallonta ya ce, "ya aka yi? Me Ummanki kuma ta miki?" Umaima ta ce, "Abbaa wai fa Banafsha ce tun ranan asabar rabona da ita, ranan Lahadi har yau litin kwata-kwata bata je boko ba, kuma ba ta je tahfiz ba, shi ne nace zan je dubota na faɗawa Ummu, har ta barni naje kuma ta ce za ta faɗa maka, amma sai Umma ta hanani, kuma ta ce idan na tafi makaranta na bi gidansu bata yafe mini ba.......", Umaima ta faɗawa Abbaa duk yanda aka yi, kaman za ta yi kuka." Girgiza kai Abbaa yayi ya ce, "Mai hali ba ya fasa halinsa, Allah ya kyauta, ki yi haƙuri ko, yanzu ki je ki jirani ina zuwa sai mu shiga gidan nasu tare, Allah ya sa tana lafiya, ki ƙyale Ummanki kar ki ce mata komai, duk abinda dai ta ce miki kiyi ko kar kiyi, idan bai saɓa addini ba kiji magananta, ita mahaifiyarki ce, kuma sai an anrabu da iyaye lafiya ake dacewa." Umaima jinjina kai tayi sannan ta tashi ta fice ta koma cikin gida, Abbaa kuwa wasta ruwa yayi ya saka jallabiyansa ya feshe jikinsa da turare sannan ya shiga cikin gidan, duk matan sannu suka masa ya amsa, sannan ya ƙira Umaima ya saka ta a gaba suka fice, suka nufi gidansu Banafsha. Ɓangaren Banafsha haka ta kwana ranan Lahadi da ciwonta, Mami sai tattalinta take yi, Alhaji ma dai tausayin yarinyar yake yi, har washe gari Litinin haka suka wuni, Banafsha zuciyanta cike da kewan Umaimatynta ga shi bata shigo ta duba ta ba, amma ta mata uzuri tasan ba zai wuce ya Danish ba ne ya hanata zuwa, sai bayan azahar Alhaji ya sallami Mami, bayan ya ajiye mata kuɗi masu yawa dan jinyan Banafsha, Allah ƙara sauƙi ya mata sannan ya fito ya shige motansa, ya nufi Yola daga nan kuma sai Kano Kanawan dabo. Sai da Mami tayi Magrib sannan ta Lallaɓa Banafsha ta yi wankanta da kanta a daddafe ta gyara jikinta chass da ita, abinci ma da lallami ta ci Mami na bata a baki, ana ƙiran isha'i Mami taje tayi sallah, Banafsha kuma tana kwance a palourn idanuwanta akan TV amma hankalinta ba ya kan TV, hankalinta na can yana tunano mata Malam Abbo nata, har Mami ta idar ta fito bata sani ba, sai da ta taɓa ta ta ce, "shalelen Mami me kike tunani haka?" Murmushi na sakarwa Mamina na ƙarfin hali na ce, "bakomai Mamina." Mami ta ce, "Ban yarda ba, amma dai ina son ki daina saka damuwa a ranki, komai na duniya mai wucewa ne, watarana ciwon nan zai barki kaman ba kiyi ba, Allah dai ya baki miji nagari Banafsha wanda zai kula mini da ke sosai fiye da ni." Ajiyan zuciya kawai na sauƙe tuna maganganun Malam Abbo, kawar da tunanin nayi tunda nasan ba mai yiwuwa bane na ce, "Mamina bansan me ya hana Umaima shigowa ba kwata-kwata, Allah ya sa ita ma lafiya." Murmushi Mami tayi ta ce, "Insha Allah! Lafiya lau take, may be wani abun ne, karki damu za ta shigo, kinsan dai Umaima na ƙaunarki." Murmushin nima na yi da na tuno Umaima, na yi shiru tare da ɗaura kai na a cinyan Mamina da ta sha nata wankan muna kallo, ba jimawa kuwa muka jiyo sallamana Umaima, daga ni har Mamina da murmushi muka amsa, hannuwana na buɗe na ce, "oyoyo Umaimatyna." Umaima rungumeni ta yi ta ce, "afuwan masoyiya." Hararanta nayi na ce, "Na janye oyoyon ma fushi nake da ke." Umaima gaishe da Mami tayi ta ce, "Tare Da Abbaa muke Mami." Washe baki Mami tayi ta ce, "To shi ne kika bar Abbaan naku a waje Umaima saboda yaranta? Ki ce ya shigo mana." Umaima miƙewa tayi ta fice, tana murmushi ta ce, "Abba ka shigo inji Maminmu." Abbaa na murmushi ya biyo Umaima da sallama suka shigo, duk amsawa muka yi, na miƙe daga kwanciyan da nayi ina murna na ce, "Sannu da shigowa Abbaanmu." Murmushi shi ma Abbaa yayi ya ce, "Sannu Faɗima." Mamina da mayafinta ita ma ta yiwa Abbaa sannu da shigowa ya amsa yana fara'a bayan ya zauna, gaishe da Abbaa nayi ya amsa, sannan na miƙe cikin dauriya, muka shige ɗakina da Umaima muka bar Abbaa da Mamina a palourn. Muna shiga ɗaki Umaima ta ce, "ki yafe mini masoyiya, na yi kewanki sosai." Murmushi na sakar mata na ce, "Nima haka Umaimatyna, wallahi kekam marana ke ciwo tun ranan asabar da dare shiyasa, kuma nasan ba zai wuce ya Danish ne ya hanaki shigowa ba, bakomai wallahi, ya karatu? Fatan dai ba'a ba da assignment ko presentation ba? Tahfiz ma normal ko?" Umaima murmushi tayi ta ce, "Nasan ai babu dalili ba za ki ƙi zuwa makaranta ba, mayyar karatu, kina fama da kanki kina tambayan wani presentation ɗin buhun uba, ni fa na stani presentation ɗin nan wallahi, amma normal ba'a ba da komai ba, tahfiz ma lafiya, Malam Abbo ya ce na ce yana gaisheki kuma yayi kewanki" ta faɗa tana kyalkyalewa da dariya. Murmushin yaƙe kawai nayi a nawa ɓangaren na ce, "Masha Allah! Ina amsawa, amma tunda ya Danish ya koma jiya Sunday, me ya hanaki shigowa da safe yau Monday?" Tura baki Umaima tayi ta faɗa mini yanda suka yi da Umma, murmushi kawai na kuma yi na ce, "Allah ya kyauta, bakomai, Allah raba mu da su lafiya." "Ameen masoyiya Banafsha" faɗin Umaima tana kwanciya a kan gadon." Wani abu na faɗa mini na faɗawa Umaima yanda muka yi da Malam Abbo, amma wani abu na ce mini a'a, sai kawai na ƙyale nayi shiru, nima kwanciyan nayi, muna hiranmu da yake ciwon maran da sauƙi. Mamina bayan mun shige ɗaki sai ta kawo wa Abbaa ruwa, bayan ya sha suka gaisa, ya ce, "kwana biyu bana ganin giftawan Faɗima fatan dai lafiya?" Mami ta ce, "Lafiya Alhamdulillahi Abbaansu, dama bata ji dad'i bane amma da sauƙi." "To Masha Allah! Haka ake so, Allah ƙara afuwa, Umaima duk ta bi ta ishi mutane da rigima shi ne nace bari mu taho tare ma." Mami dariya ta ɗan yi ta ce, "Yaran nan ai rigimansu ya fi ƙarfinsu, ita Banafsha ma tana kwance tana fama amma sai mita take wai Umaima bata shigo ba yanzu ma mun gama maganan kenan sai ga sallamanta." Abbaa murmushi yayi ya ce, "Masha Allah! Ai haka ake so, Allah ƙara haɗa kawunansu, kinga sai a bar miki su ki haɗa duka biyu." Mami ta ce, "Waii! Wane ni, ai Ummu ba za ta bar mini yarinyarta ba, da dai za'a ce a haɗa mata su ne ita za ta yarda." Dariya Abbaa yayi suka ɗan taɓa hira da Mami sosai da yake daman can sun ɗan mutunci, Abbaa mutum ne da bai da damuwa sam-sam, da yayi tunanin baje wa Mami sirrin ƙalbinsa amma sai ya fasa ya bari zuwa gobe, tunda yanzu dubiyan Banafsha suka zo. Sai da suka ɗan ɗau lokaci sannan Abbaa yayi ƙiran Umaima ta zo su koma, amma rigima ta saka ita za ta kwana, ba musu Abbaa ya ce su kwana lafiya ya juya yayi tafiyansa bayan sun yi sai da safe da Mami, Umaima da farinciki suka fito da Banafsha suna kallo duka da Mami har dare tayi suka wuce suka kwanta, Mami ma tayi nata ɗakin ta kira Alhajinta suna wayansu cikin soyayya tana masa sannu da hanya dan ya koma gida. Abbaa yana komawa dai Umma sai zubawa bayansa ido ta ke ta ga ɓullowan Umaima amma shiru, daganan ya fahimci inda suka je, wato Umaima faɗawa mahaifinta tayi shi ne suka je tare, daman mai neman kuka ne aka jefe sa da kashin akuya, ya ce zai auro karuwa ga shi ya samu daman zuwa zance ma dan cin fuska, ƙwafa Umma ta yi ta ce, "Idan na kamaki Umaima sai ɗan buzunki." Ummu kuwa ta tambayi ina Umaima ya faɗa mata ya baro ta gidansu Faɗima, Ummu ta tambayi ya jikin nata, ya amsa da sauƙi, ta ce ita ma gobe za ta je dubo ta, Abbaa ya ce, "Ba damuwa Allah ya kai mu, Kinga sai ki raka ni zance mu dai-daita, tasan da amincewnki, dan inaga idan ba ki ce kin amince ba, zai yi wuya ta yarda saboda kar ta ci amanan ƙawance." Dariya Ummu tayi ta ce, "Allah ya kai mu Abbaansu." Sai da safe ya yiwa Ummu ya wuce ɗakin Umma da yake ita ce da girki. Washe-gari da safe Umaima daga gidan Mami ta shirya ta je tahfiz, bayan anyi karatu an tashi Malam Abbo ya kuma tambayanta, ta faɗa masa bata jin daɗi ne amma da sauƙi, hamdala yayi tare da yi mata addu'an samun sauƙi, sai yanzu hankalinsa ya kwanta, kuma yana kan lissafi sati guda ranan asabar nayi zai koma ya kuma jin hukuncin da ta yanke, Umaima kuwa tana dawowa ta kuma shiryawa daga gidan Mami ta wuce school ta saka uniform na Banafsha, ko da ta dawo bata tafi gida ba har sai da Ummu ta shigo, bayan sun gaisa da Mami ta tambayi jikin Banafsha Mami ta amsa da sauƙi, sannan ta saka Umaima a gaba suka koma gida, bata haɗu da Umma ba daga nan ta shirya ta koma tahfiz na yamma. Abbaa yau ma bayan ya dawo ya shirya tsaff ya nufi gidan Mami dan ya sanar da ita abinda ke ransa. Alhaji Mukhtar ya koma gida lafiya, ya samu Hajiya ta tafi Dubai akan business nata, gaba-ɗaya ya ji ba daɗi amma yayi haƙuri yana addu'an Allah sa ta gyara halinta, Allah kuma ya mallaka masa Ramla. Yana zaune a palourn sama yana ayyukansa a system nasa, Majeeder ta shigo da sallama, amsawa yayi yana murmushi ya ce, "zauna Maman babanta." Majeeder zama tayi ta gaishe da Alhaji sannan cikin shagwaɓa ta ce, "Papi ni wallahi na gaji, gida kullum shiru, dan Allah nima a mayar da ni gidan Affa General." Alhaji barin abinda yake yi yayi ya shafa kanta tare da kamo hannunta ta zauna a kusa da shi, yana murmushi ya ce, "Mai jiddan babanta kina so idan kika tafi na zauna ni ɗaya ne nima? Kina son damuwa ya yiwa babanki yawa? Ke nake gani a gidan nan naji sanyi a rai na, ki yi haƙuri ko, in Allah ya yarda komai zai wuce, na kusa kawo miki Aunty da kuma ƙawa abokiyar hira, ba dai kina son ƙawa ba?" Gyaɗa kai Majeeder tayo ta ce, "Eh Papi ina so." Murmushi yayi ya ce, "yauwá na kusa kawo miki ƙawa, kuma auntynki har da ƙanne za ta haifa muku, Mami za ki dinga ƙiranta ma, ƙawarki kuma sunanta Faɗima amma ana ce mata Banafsha, ita ma ta sanki, kuma tana son ƙawance da ke, su ma da suka yi musabaƙa a makarantar su ita ce ta zo ta ɗaya kaman yanda kika zo ta ɗaya." Majeeder da murna da farin ciki ta ce, "Wayyo Papi ina sonta sosai, dan Allah a kawo su da wuri, nima a mini ƙanne, ka ga sister Ramla ma da ƙannenta, Suhaila da Nabeela." Alhaji dariya yayi ya ce, "kinsan me Maman babanta?" *** Masu Sharhi ina godiya, waɗanda basa yi ma na gode amma dan Allah a ƙara himma, kunga jiki da jini sai a hankali sharhinku ke bani ƙwarin guiwan yin typing balle yanzu da bana jin daɗin jikina sai a hankali, Uwar batoorl taku ❤️ masu daraja habibties. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Ɓingel kabi Heartbeat Hafsat Umar Habiba muhammad Yusuf اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 Ba editing ayi haƙuri da typing errors. 🅿️ 51 _ 55 Majeeder girgiza kai tayi ta ce, "A'a Papi." Alhaji ya ce, "Sunan Maminki ke da ƙawarki ne Ramla, dan haka ki daina ƙiran sunan kinji." Jinjina kai Majeeder tayi, tana murmushi ta ce ta daina, Alhaji ya ce, "good girl, kuma su General ɗin ma suna zuwa in Allah ya yarda nan da next week, inyaso idan kuna hutu a school ba lectures sai ki je can ki yi hutunki, saboda nima zan yi tafiya kuma zan iya kai 2 month's kamun na dawo." Majeeder washe baki tayi ta ce, "Allah ya kai mu lafiya, Allah kai ka lafiya ya dawo da kai lafiya, Allah kawo su yaya lafiya, finally zan ga yaya Bunayd bayan stawon lokaci, gaskiya ni Papi ka faɗawa yaya idan yayi aure ni gidansa zan koma da zama" ta ƙarishe maganan kaman za ta yi kuka. Alhaji murmushi yayi ya ce, "Idan kika koma gidansa ke kuma wa zai zauna miki a naki gidan? Maman babanta." Majeeder tura baki tayi ta ce, "Ni dai Papi sai na koma gidan yaya da zama." Alhaji ya ce, "Shikkenan Allah basa mace tagari, sai kuma ki masa magana ki ce yayi aure, ni kuma sai ma faɗa masa za ki koma gidansa da zama ko?" Majeeder na murmushi ta gyaɗa kai, hira Alhaji ya dinga janta da shi har bacci ya ɗauketa a wajan, tashuwa yayi ya gyara mata kwanciyanta, sannan ya ci-gaba da aikinsa hankali kwance, cike da kewar Ramlatunsa. ⭐ CAS Bunayd mancewa yayi da maganan zuwa Kano, ya shirya ya bar Nigeria, daman shi kaman network haka yake ba tabbatas, yau yana Nigeria gobe kuma yana wata ƙasar, musamman ma da yake Sojan sama, kuma yawancin ƙasashen da yake zuwa yana da gida a can, kuɗin gaske Bunayd yake da shi, ko iyayensa ba su kai sa kuɗi ba. Yau kuma a ƙasar Spain ya sauƙe zangonsa, jirginsa na sauƙa drivernsa ya zo ya ɗauke sa, a gaban wani tankamemen gida motan nasu ya staya, da wani button ake buɗe gate na gidan, ana buɗe musu suka shiga, mota na parking Bunayd ya buɗe da kansa ya fito, cikin takunsa na isa ya ƙarisa bakin ƙofan shiga gidan, ƙofa ne mai amfani da numbobi (password) wajan buɗewa, sai da ya saka sannan wani murya kaman na yara ya ce, "welcome" ƙofan ya buɗe ya shige. Subhanallahi! Gida ne na gani na faɗa, stayawa faɗan staruwan gidan da haɗuwansa ma ɓata baki ne, direct ɗakinsa ya wuce ya wasta ruwa ya sauya wasu haɗaɗdun kayan sannan ya fito, a babban palourn ya samu wata dattijuwar baturiya ɗauke da tray, cikin turanci ta gaidasa, Bunayd ya amsa mata ba yabo ba fallasa, faɗa masa tayi ga abinci, lumshe ido yayi kawai bai ce komai ba, saboda ya sha faɗa mata tabar wahalar da kanta masa girki ko ya zo, indai yana buƙatan abu zai mata magana, amma dattijuwar muddin ya zo ƙasan to sai ta masa abinci, faɗa mata yayi ya ƙoshi sai ya dawo zai ci, yana gama faɗa yayi gaba, a wata haɗaɗɗiyar mota baturen drivern nasa ya ja sa suka tafi inda ya faɗa masa. Wani irin haɗaɗɗen wajan shaƙatawa ne, ba abin da babu a wajan, gefen eatery, club, bar, hotel, swimming pool etc. Bunayd wajan pool ɗin ya nufa, irin kujera mai kama da resting chair haka nan ya samu ya zauna, matan turawa sai zirga-zirga suke, daga masu swimming-wear sai masu pant da bra kawai, Bunayd kallon ma na rigima da isa yake yi, idan ya kalli wannan ya taɓe baki, idan ya kalli wannan ya runste ido, idan ya kalli wannan ya yi murmushi kawai, wayansa ya ciro tare da dialing layin general, a ɓangaren General daman ya gama gwada layin Bunayd na Nigeria bai shiga ba, rasa layin wacce ƙasa zai fara ƙira yayi, sai kuma ga ƙiran Bunayd ɗin ya shigo, amsawa yayi yana murmushi ya ce, "ɗan halak ya ƙi ambato." Murmushi ƙayatacce Bunayd yayi ya ce, "Affa Barka da gida." General ma murmushin yayi ya ce, "Yau kuma kai ne da ƙiran Affa? To ban amsa ba ka faɗa General ya fi daɗi, Affa haka kaman wani stoho, General ya fi ana ji ansan matashi ne ni ba stoho ba." Bunayd murmushi yayi sosai har sai da fararan haƙoransa suka bayyana, dimples nasa suka losta, cewa yayi, "Affa ai daman kai ba stoho bane, Sir ne dai stoho." General ya ce, "Yaya dai ya ce ka daina ce masa Sir, yauwa daman yanzu nake ƙiran layinka naji shiru na ce ka tafi kuma." "Eh amma 2 day's kawai zan yi na dawo, akwai abinda na zo yi ne mai muhimmanci." General ya ce, "ai ko yawonka ma mai muhimmanci ne kai kam my Man, yanzu dai ka tabbatar ka dawo nan da kwana biyun saboda tare nake so muje Kano dukanmu." Dafe kai Bunayd yayi ya ce, "Ni na manta ma ai General, amma dai gobe zan dawo in Allah ya yarda, daman auren Abeed ma ya kusa may be na zauna har a yi bikinsa." "Ok! Allah dawo da kai lafiya Man, daman nasan yawo ka je ba aiki ba, kai ai ko stunstu ya ganka haka ya ƙyaleka, Allah ya sa ka haɗu da taka matar a wajan auren Abeed ɗin." Murmushi kawai Bunayd yayi bai ce komai ba, ci-gaba da wayansu suka yi kaman abokanaye ba uba da ɗa ba, sai da suka gama suka yi sallama ya kashe wayansa, wata baturiya ne ta zo wajan tare da miƙa masa sabbin kaya a ledansu, amsa yayi ya je ya sauya ya zo ya shige ruwan shi ma, tunda ya shiga ƴammatayen ciki suka fara yiwa wa kansa, Bunayd murmushin mugunta kawai ya yi dan shi kaɗai yasan abinda zai yi, wayansa da ke wajan kujera ne ya ɗau suwwa, drivernsa da ke staye a gefe shi ya miƙo masa, kara wayan yayi a kunnensa ya ce, "ina pool Abeed, idan na gama zan ƙiraka." Dariya Abeed yayi ya ce, "CAS ka ce kaje bawa idonka abinci, musulmin ɗan jagaliya ba, kai daga can sai can, kuma duk ka gama yawo ka dawo ka ce matan ba su gama sanin duniya ba, to nidai maganan serious ne kawai mu yi ta yanzu ba wani sai ka gama, inba dai Chaji kake yi ba." Ɓata rai Bunayd yayi ya ce, "Amma dai ka gama da ni wallahi, yanzu har akwai macen da za ta iya mini Chaji a Spain? Ƴan banzan da duk Palace nasu yake a salafce ba ɗumi, zan je ina Chaji ina gane akwai mutane a duniya ne, ai full definition of Chaji shi ne wanda kana yi baka sanin kowa yana existing, duka matan Spain ƙauyawa ne, yanzu ma so nake na ɗura wa wata ruwa." Dariya Abeed yayi sosai ya ce, "To ko ba Palace kake Chaji ba nasan ko kana taɓa biyu kyauta milkies." Guntun tsaki Bunayd ya ja ya ce, "Duka matan Spain ƙwailaye ne, ba wacce milkieynta yayi girman da zai ishi CAS Bunayd, wasunsu ƙirjin ma kaman an shafe sa, abu kaman ƙwallon cashew, da dai akwai mai kaman Mango ko Orange ai na iya lallaɓawa, amma duk abu ba kyawun gani, kuma fa yanda suke yawo hakan nan gani suke sun ƙure adaka suna da kaya load-load back an front, kai Allah mun gode maka, kuma mun tuba, Alhamdulillahi da ba mu fito a cikin turawa ba, haba dan Allah sai kaga mace kaman boss a dire kawai ba shape, baya ba tudu ƙirji ba tudu, daga kyawun fiska har na sura ana cire matan larabawa da na indiyawa to sai matan Africa, ni kwata-kwata turawannan ba burgeni suke ba, ƙauyanci ya musu yawa basu waye yanda ya kamata ba, bari na ɗurawa wata ruwa zan ƙiraka" Bunayd ya faɗa lokacin da ya ji wata na shafasa. Abeed dariya yayi ishashshe ya ce, "Baka da kirki, nasan ba zai wuce an ɗan rungumeka ka ji ɗumi ba, ka ci-gaba da dannawa beb's na mutane ruwa a pool, wataran sai ka kashe wata saurayinta ya ɗaureka, bar ganin kai Soja ne, law's na ƙasashen turawan nan sam bai da daɗi, ba tausayi ba sassauci mugaye ne." Taɓe baki Bunayd yayi ya kaste ƙiran, Abeed a nasa ɓangaren dariya ya dinga sha, ya zauna jiran Bunayd ya gama muguntansa su yi waya ya faɗa masa abinda ake ciki. Bunayd juyawa yayi ga baturiyan da ke shafa sa, murmushin mugunta yayi a zuciyansa ganin wata guzuma ce fiska ko kyan gani babu, a fili kuwa stadadden murmushinsa mai rikata mata ya sakar mata, tuni baturiya ta susuce tana ta shafa jikin Bunayd, cikin turancinta ta ce, "tattoo naka yayi kyau handsome." Lumshe narkakkun idanuwansa yayi, sannan ya buɗe su kaman mai jin bacci ko mugun feelings, a hankali ya mosta bakinsa ya ce, "thanks." Baturiyan kuwa ƙara matowa tayi akan Bunayd tuni ta rungume sa, Bunayd ganin tana ƙoƙarin taɓa masa Dragon ɗin sa, tuni yayi cikin ruwa da ita, Bunayd mayen ruwa ne, sosai ya iya ruwa kaman ba sojan sama ba, baturiya duk iya ruwanta sai ga ta kaman za ta mutu dan haɗiyan ruwa, saboda Bunayd yi yayi kaman shafata yake amma danneta yayi a cikin ruwan kuma bai bari ta ɗago ba, sai da ya ga tana ƙoƙarin mutuwa sannan ya saketa yayi gaba, a mugun haukace ta ɗago ta fice a ruwan tana ƙaƙarin amai. Bunayd kaman ba shi yayi wannan ƙetan ba ya juya ya cigaba da swimming nasa, kuma duk macen da ta taɓa sa, in dai ya kulata to sai ta sha ruwa dai-dai gwargwado, kuma yana gamawa zai yi gaba, sai da ya gama iyayinsa sannan ya fice ya amshi towel ya goge jikinsa, kayansa ya mayar suka yi gaba, suna komawa gida ya taba girkin dattijuwar kaɗan ya haura sama ɗakinsa, yan shiga ya faɗa kan gado yana sakin dariyan mugunta, kar ku so ganin irin kyawun da dariyan ya yiwa Bunayd, a fili ya ce, "Ai ba mai taɓa jikin CAS Bunayd a bati sai mai Palace da ɗumi, mai isassun milkies." Yana gama dariyansa ya ƙira Abeed, tunda Abeed ya ji muryan Bunayd ya tabbatar ya aikata muguntan nasa, shi ma dariyan yayi ya ce, "kama tu dini tu dana, kana wahalar da budurwayen wasu, kai ma Insha Allah wani na can yana wujijjiga matar da za ka aura, may be ma har Palace ɗin ya leƙa." Taɓe baki Bunayd yayi ya ce, "So what!? Ai ni banda mastala da virginityn mace, abinda nake buƙata kawai mace wacce tasan rayuwa, idan wani ya leƙa Palace ɗin ma aiki ya rage mini no delay, Palace na isowa gare ni kullum Chaji available, kullum full cherge kawai, mace nistasttiya ba ta cikin tsarina, so ban saka virginity a starina ba, i want and love her, not her virginity, idan kai ma dan budurcin za ka auri salihar taka tun wuri ka sanja mind, Allah na iya jarabtan mutum duk kamewansa sai ya auri mace ba kamammiya ba, idan ka saka virginity a ranka to idan baka samu ba hakan na nufin auren ba lasting zai yi ba, dan haka tun wuri ka gyara niyanka akan maganan aure, ni shiyasa na jima da saka wa rai na, ƴar jagaliya iri na zan aura, ko wacce ma ta fi ni shaƙiyanci, ba zan auri kamila na cuceta ba, nafi son tantiriya-tantiriya haka yanda nake a gantale ita ma ta zama dai gantalalliya-gantalalliya sai mu zauna normal, wasu mata ba sex ke sa su rasa virginity nasu ba, akwai hanyoyi da yawa da suke rasa virginity ɗin su ta shi wanda wasu ba su sani ba ko kuma ba da son ransu ba, wasu situation na rayuwa ko kuma iyayensu basu da hali, musamman masu ɗaukan abu mai nauyi, sannan ga wannan bala'i da ke damun mutane na infection, shi ma idan ya yiwa mace yawa ai ya isa yayi disvirging nata musamman yaran talakawa masu using local toilet, so ka gyara niyanka." Abeeb murmushi yayi tare da yin kabbara ya ce, "Allahu Akbar! Sheikh CAS Bunayd bin Mukhtar sule kwalli." Bunayd da har yanzu fiska ba'a sake ba ya ce, "Me yasa ka ƙirani dama?" Abeeb murmushi yayi dan yasan abokin nasa kuma yayi fushi, maste dariyansa yayi ya ce, "auren ne an dawo da shi baya, 3 week's wai, and next week zan tafi Adamawa za'a tura mu wani local government Michika, kuma ina tunanin za mu iya kai 2 to 3 week's a can, so za ka yi handling na abubuwan da ya shafi bikin ne, sai ka shigo Kano da wuri." CAS Bunayd ya ce, "All the best! Za mu shigo next week da su General duka, dama na faɗa masa zan zauna har bikinka, so idan busy ya bar ni ba mastala komai normal, ango na saliha kamila, Captain Abeed ya kusa dangawa ga Palace, Dragon za'a sha Chaji." Dariya Abeed ya fashe da shi bai shirya ba ya ce, "ɗan iskan abokina, Allah nuna mini taka matar, tun a waje zan faɗa mata gaskiya kada mu munafurceta, kai iskancinka har da na sayarwa kuma dai da alama kai jarababbe ne." Murmusawa Bunayd yayi ya ce, "Ko banda jaraba ai sadaki ya fi kuɗin da ake bawa ashawo, idan ban da shi ma zan koyo." Waya suka yi har suka yi sallama kaman ba komai, dan Bunayd duk fushinsa yana da saurin sauƙa kuma bai da riƙo. Abubuwan da ya kamata yake yi har dare tayi, nan ma ya shirya driver ya ja sa sai club, Bunayd fiska a haɗe ya shige, duk wata mace da ta tinkaro sa to tana kallon fiskanta take shan jinin jikinta, Bunayd ya iya rawa na fitan hankali, tunda ya hau step na guy's ɗin, to duk wani mai rawa tsayawa yake kallon na Bunayd, mata sai gani sai hange daga nesa dan fiskan nan a haɗe ba alaman rahama, gaba-ɗaya wajen tafi ya ɗauka, wasu mazan turawan kuwa kishi suke suna haushi a banza, saboda Bunayd bai san suna yi ba ko a kwalansa, sai da ya gama shashewansa sannan ya samu waje ya zauna, abubuwan sha aka kawo masa, duk wine sun fi yawa, taɓe baki yayi saboda shi ko non-alcoholic wine ba ya sha, drivernsa ya turawa text ya ɗauko masa energy drink a mota ya kawo masa, sai da ya kwankwaɗa ya ɗan ƙara cashewa sannan suka koma gida lokacin kusan 12 na dare agogon Spain. Suna komawa ya wasta ruwa tare da ɗaura alwala, dama Bunayd ibada ba ya wuce sa, mayen ibada ne sosai-sosai, ko me yake lokacin sallah na yi zai yi, kuma nafilfilu ma haka yake yin su kaman wani babban Malami, yanzu ma sai da ya gabatar da nafilfiulunsa har 1 da mintuna na dare, sannan ya bi lafiya haɗaɗɗen gadonsa ya kwanta. Washe-gari da wuri ya shirya cikin court nasa arsh color, ba ƙaramin kyau kayan ya masa ba, ka ce ma'aikacin banki ne, yana fitowa dirver ya ja su, motoci uku ne, ɗaya na guard's nasa a gaba sai wanda yake ciki a tsakiya sai kuma wani a baya, a gaban wani kantamemen building mai hawa-hawan gaske suka yi parking, guard's ne suka buɗe masa ƙofa ya fito yana takunsa na sadaukan maza, wani ɗan ƙaramin brief case ne a hannunsa ya shige ciki, lifter ya hau ya kai sa step da zai je, a wani haɗaɗɗen office ya tsaya aka basa izinin shiga. Office na wani babban ɗan kasuwan Bature ne, bayan Bunayd ya zauna ya zaro wasu peppers ya miƙawa Baturen, sosai suka tattauna kuma da alama dai kaman contract na wani aiki ne, sai da suka gama ya fice, bayan sun koma gida ya shirya sai airport, daganan sai Nigeria, ko da ya dawo sai da ya huta sannan ya tattara komai da zai buƙata sojojin suka shigo suka ɗauka suka fice. Yau ma da jerin motoci kaman kullum haka suka fice a gidan da mugun gudu suka yi Victoria Island, suna isa aka buɗe masa ƙofan motan, yana ƙoƙarin fitowa sai ga wani kyakkyawan yaro wanda ba zai wuce 14 year's ba ya zo yayi hugging nasa, Bunayd na murmushi ya ce, "Nabeel kai ne ka girma haka?" Nabeel murmushi yayi kawai ya amshi kayakin Bunayd da ke hannun sojojinsa, suna tafiya suna hira, Nabeel ya ce, "Yaya zama Soja is not easy gaskiya, ni kawai ka yiwa General magana nima a barni na tafi ko Spain ɗin ne ko Turkish nima na karanto wani abun." Bunayd murmushi yayi dai-dai sun shiga palourn gidan, wani corridor suka bi sai ga su gaban wani parta haɗaɗɗe, shigewa suka yi Nabeel ya dire kayakin a palourn ya ce, "Yaya CAS ɗan gidan General ya dawo, nidai ka taimaka ka masa magana, nasan idan kai ne ka yi magana zai yarda." Bunayd ya ce, "tunda ka dawo za mu yi magana letter, yanzu dai bari na huta, sai ka faɗawa su Suhaila su shirya tafiya Kano, kai ma har da kai, General ya ce duka gida za'a je, ina tunanin Suhail ma may be zuwa gobe yana hanya." Sanin Bunayd baya son hayaniya idan ya ce zai huta, sai Nabeel ya fice salun alun, dan ba laifi idan Bunayd ya so surutu to ko menene biye musu yake yi, Nabeel na ficewa Bunayd ya rage kayan jikinsa a nan palourn ya kwant dan ya huta, baccin ne bai ɗauke sa da wuri ba, can yayi ɗan guntun staki a fili ya ce, "Kowa yayi sa'an Mom amma ban da mu, na stani zuwa Kano ba dan kowa ba sai dan ke Mom.." haka ya dinga mitan surutu shi kaɗai har bacci yayi gaba da shi, Bunayd fa da alaman birgima ne da shi dan kaman zai faɗo daga kujeran haka yake baccin.🤣 ⭐ Banafsha da Maminta suna zaune a palournsu suna hira, sai Banafsha ta dubi Mami ta ce, "Mamina tunda ba ki saya mini waya ba ki saya mini system to." Murmushi Mami tayi ta shafa kai na ta ce, "shalelen Mami kada ki damu ko, Allah ya kawo kuɗi Mami za ta saya miki abinda ya fi system ma balle ƙaramin alhaƙi waya, duk abinda nake yi dan ke nake yi, neman kuɗi da komai faɗi tashi duk saboda gudalliyan Maminta nake yi, Faɗima ƴar albarka." Tura baki nayi jin wai Mamina dan ni take komai, yanzu ba abun na ce idan saboda ni take wannan rayuwa mara fa'idan to ta bari na yafe ba, amma nasan sai ma Mami ta dakani duk da banda lafiya, jan bakina nayi tare da yin shiru, can na miƙe na ce, "Mami bari na sauya pad." "To ammatan Maminta a fito lafiya", Mamina ta faɗa tana murmushi, ni kuma na shige ɗakina cikin jin kunya. Banafsha na shiga ɗaki bai jima ba sai ga sallaman Abbaa, Mami da fara'a ta amsa tare da masa iso, wucewa ɗaki tayi ta sako mayafi sannan ta dawo suka gaisa cikin mutunta juna, Abbaa ya tambayi jikin Banafsha, Mami tana murmushi ta ce, "Da sauƙi sosai ma, yanzu ta tashi ta shiga ɗaki." Abbaa yana murmushi ya ce, "To Masha Allah! haka ake so." Palourn sai ya ɗau shiru na mintuna daga Abbaa har Mami ba mai magana,can Mami sai ta miƙe tare da cewa, "Bari na ƙira maka Faɗiman tunda ta shiga ɗaki ta zauna shiru." Abbaa na maza yayi ya daure saboda Mami sosai ta masa kwarjini, cikin jarumta ta ce, "A'a ƙyaleta ta huta, daman dai wajanki na zo." Mami murmushi tayi tare da komawa ta zauna, bata kawo komai a ranta ba ta ce, "Allah ya sa dai ba laifi na yi ba." Abbaa murmushi yayi ya ce, "ai kuwa laifi kika yi, irin gungumemen laifin nan, dan ko a kotu ya wuce civil case sai dai a ƙira sa da criminal case." Mami ɗan waro ido tayi ta ce, "ahh! Ba sai an kai ga kotu ba ma, haƙuri zan bada, yanzu dai a faɗa mini laifin nawa na ji sai na bada haƙuri yanda ya kamata" ta faɗa tana murmushi. Abbaa gyara zama yayi tare da gyaran murya ya ce, "Ai haƙuri ba zai goge wannan laifin ba, saboda criminal issue ne, sata kika mini irin babban satan nan da idan aka riga aka maka shi sai abinda Allah yayi kawai." Mami da bata harbo jirgin abinda Abbaa ke nufi ba, da mamaki ta ce, "haƙuri kuwa ya zama dole na bada, Allah baka haƙuri Abbaansu, me na sace haka nayi gaggawan dawo da shi?" Abbaa murmusawa yayi ya ce, "ai sacewan shi ne dai-dai Mamin yara, idan an sace ba'a dawo da shi sai dai a riƙe da kyau, Mamin yara maganan gaskiya da gaske nake kuma da gaske nazo sannan a shirye, a taimaka wa bawan Allah a kula mini da zuciyata da aka sace, tun ranan farko da na fara ganinki naji kin kwanta mini a rai kin mini, kin tafi da imanina, na daure na kusan shekaru goma sha, amma yanzu abin ya fi ƙarfi na a taimaka mini a tausaya mini, da gaske kuma na zo idan kin amince ko juma'an nan ban ƙi a kawo mini ke gidana ba, kuma kada ki yi tunanin alaƙanki da Ummul-khultum, domin ban zo ba sai da duk suka amince suka kuma yarda, dan Allah ki taimaki marayan Allah mai mata biyu, na jima ina dakon soyayyanki Hajiya Ramla." Mami tunda Abbaa ya fara magana ta ɗauke wuta na ƴan mintuna, zamowa tayi kaman photo kawai tana kallonsa ta rasa ma me za ta ce ko me za ta yi, mamaki kawai ya tafi da ita a zaune, kallonsa take kuma ba ta ko kiftawa, har ya gama magana bata iya mosta laɓɓanta ba balle ta ce wani abu, dan bata san ma me za ta ce ba. Abbaa murmushi ya sakarwa Mami ganin ta kafesa da kallo, a hankali ya ce, "Hajiya Ramla ke na ke saurare." Mami wani irin dogon ajiyan zuciya ta sauƙe, sai sannan ta kawar da idonta a kan Abbaa, wani irin murmushi ta saki tare da buɗe baki ta ce... # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Ashe zamu ga juna fan's club Adamsy fan's club Sarauta's Library Asmabaffa official novels Fan's masu Sharhi a wannan groups, Uwar batoorl na godiya, wannan page naku ne. اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 Ba editing ayi haƙuri da typing errors. 🅿️ 56 _ 60 Mami ta ce, "Alhaji abinda kunnuwana ke jiye mini kana faɗa haka ne ko kuwa mafarki nake?" Abbaa yana murmushin ya samu karɓuwa ya ce, "ba mafarki kike ba Mamin yara haka abin yake, nine dai na ce a taimaka mini a tausaya mini kar na mutu da soyayyanki, kuma ko nan da sati kika buƙaci ayi biki to a shirye nake." Mami murmushin yaƙe wanda ya fi kuka ciwo tayi sannan ta ce, "ka yi haƙuri Alhaji ba wai na ƙi ka bane, a'a aure ne kawai ba ya gabana har yanzu, wanda nayi a baya ya isheni." Abbaa cikin damuwa yake kallon Mami ya ce, "Me yasa Hajiya Ramla? Ki faɗa mini gaskiya idan nine ban miki ba ko kina tunanin wani abu ne akan mata na." Girgiza kai Mami tayi tana mai iya ƙoƙarinta wajan ganin wannan magana bai sa ta yiwa Abbaa rashin mutunci ba ta ce, "Ko ɗaya Alhaji, nice kawai ba aure a gabana." Abbaa ya ce, "Duk ɗan sunna ai ba ya ƙin aure Mamin yara, nasan dole dai kina da wani dalilin naki, Allah huci zuciyanki amma dai ina sonki, kuma zan baki lokaci dan jiran amsar da za ki bani, yanzu ban ɗauki wannan a matsayin amsa ba, daganan har wata guda na baki duk ki yi shawara ki yi tunani, duk abinda kika yanke ki sanar da ni, musamman in maganan bikin ne to sati guda kawai za'a yi Insha Allah sai ki fara shiri tun kamun ki gama tunanin" Abbaa ya faɗa yana sakar wa Mami murmushi ƙayatacce. Gululun baƙin ciki ne ya tokare Mami, amma da yake bata son dogon magana sai bata ce wa Abbaa komai ba, har ya gama iya surutunsa ya fice, sai sannan ta ja wani dogon tsaki a fili ta ce, "Matarka bata ƙyaleni ba kuma ba ta ƙyale yarinyata ba a haka zan aure ka? Ai ko auren zan yi ina da wanda nake ƙauna, shi ma ban amince masa ba balle kai, saboda ba auren bane a gabana yanzu, kuma iya shekarun da ka ɗauka kana dakon soyayyata haka Alhaji Mukhtar ya ɗauka ko na ce fiye da haka, dan tun Banafsha bata yi wayo ba ga shi har ta zama budurwa, wa ma ya san ko kai naka na yaudara ne kawai, ni yanzu ba aure ne a gabana ba, aurar da Faɗimatu na shi ne a gabana, Allah kuma ya bata miji nagari..." Haka Mami ta dinga mita da surutu ita kaɗai kaman wacce ke yi da mutum a gefenta, ko kuma wacce aka kunnata, hhh ko da yake Abbaa ne ya kunnata tunda ya taɓo mata inda ke mata ƙaiƙayi. Banafsha da ta shiga ɗaki sanya pad, tun shigowan Abbaa ta ji, da har tana niyan fitowa amma tun daga kalman Abbaa na Mami ta masa laifi har ya ce criminal case ne, sata ta masa tuni Banafsha ta fahimci me Abbaa ke nufi, mamaki ne da kuma farinciki suka kuma kama Banafsha san da Abbaa ya furta abinda ke zuciyansa, duk da a wani gefe tana tuna Umma da Ya Danish, amma abin ba ƙaramin daɗi ya mata ba, kuma ya ƙara wa Abbaa kima a idonta, Abbaa shekara da shekaru yake maƙwabtaka da Maminta, yasan abinda take aikatawa amma duk da haka yana sonta, kuma bai yi ƙasa a guiwa ba yau ya sanar mata sannan a shirye yake da ya aure Mami akan lokaci, su Abbaa na hiransu amma Banafsha ke musu murmushi ita ɗaya kaman ta buga tsalle, saboda haka kawai ita ta ji Abbaa ya fi kwanta mata akan Alhaji, musamman da za su zama so close again da Umaimatynta, kuma tunda su Ummu sun amince su shikkenan ba komai Allah ya sa Mami ma ta amince... Tunanin Banafsha na Allah sa Maminta ta amince ne ya staya, sakamakon jin amsan da Mami ke bawa Abbaa, saurin runste ido Banafsha tayi tana jin kaman ita ake sokawa wani abu mara daɗi a kirjinta, gaskiyan Abbaa ne da ya ce duk ɗan Sunna ba ya ƙin aure, kuma a ganin Banafsha ko yana da dalili duk da haka ƙin aure bai kamace sa ba, saboda yanda aka same shi ta Sunna, to bai kamata a ce shi ma bai da wannan burin na samar da wasu ta Sunna ba, menene mastalan Mami kam? Allah ya hore mata baiwan kyawun jiki, fiska, hali da na zuciya, sannan uwa uba abinda wasu sai sun haɗa da boka da malam suke samu, to ita Allah ya hore mata a sauƙi wato farinjini, Mami na da jama'a sosai-sosai, amma Banafsha har yau ta rasa ne ya sa mahaifiyarta ta zaɓi wannan rayuwan, dole tana buƙatan amsa, dole tana buƙatan jin labarin wacece Maminta, asalinta, ƴan uwanta, mijin da take ikirarin ta yi auren farko ta gama, da duk komai ma dangance da tarihin rayuwan baya na Mami, a hankali Banafsha ta lumshe ido ta ce, "Duk a ina zan samo waɗannan amsoshin ya Rabbi, ka iya mini da kanka ya Hayyu ya Ƙayyum" ta faɗa kaman za ta fashe da kuka(ni uwar batoorl na ce ni ke da amsoshin Banafshaty, ki biya kiji komai a_z).🤣 Banafsha dai-daita nistuwanta tayi yanda Mami ba za ta gane ta ji abinda suka tattauna da Abbaa ba, ta shiga palourn da sallama, jikin Mami ta koma ta kwanta tana cewa, "Mamina kaman muryan mutun na ji, amma kamun na fito ban ga kowa ba ke ɗaya." Mami taɓe baki tayi ta ce, "Eh! Abbanku ne ya zo tambayan ya jikinki, na faɗa masa da sauƙi, zan ƙira ki kuma ya ce sauri yake, idan kin ji sauƙi sai ki shiga gidan ki gaishe sa ko." Jinjina kai na yi a zahiri, a zuciyata kuwa mamakin Mamina nake, mamakin gaske ma kuwa, wato Mami ba za ta ma faɗa mini ba, ana cewa yaran fari abokanan shawara ne kuma ƙawaye amma banda Mamina, musamman a irin wannan magana, uhmn to Alhamdulillahi!, Duk da nasan maganan da ta yi ɗazu da ɗan gaskiyanta na Umma bata ƙyaleta ba kuma ba ta ƙyale ni ba, amma wannan ba hujja ba ne, ko ni da ya Danish yayi ƙoƙarin ƙeta mini mutunci na so mata auren Abbaa balle ita da bata san da wannan ba ma, kuma Mami in za ta duba da kyau ni a ganina auren Abbaa ya fi mata auran Alhaji, tana son Alhaji kam amma wani lokacin abinda muke so ba shi ne alkairi a gare mu ba, sannan tana maganan aurar da ni, a muna zaune haka ba namiji shi ne take tunanin wasu za su zo neman aurena wajanta tana mace? Ai babu mai aurar mara uba, ana dai auran wacce/wanda ba su da uwa amma banda marassa uba, saboda da uba ake ado ba rigar aro ba, ni sai yanzu ma Malam Abbo ya faɗo mini a rai, Mamina bata nadama a irin wannan rayuwan ina na isa na yi maganan aure, shiyasa ma ni ban saka wa rai na zan yi aure ba, tunda haka Mamina ta zaɓa sai mu zauna duka haka, niyan nayi shiru nayi mu je a haka a bansan abinda ke tafiya ba, amma zuciyata ta ƙi ƙyaleni nayi shiru, numfasa nayi a hankali kaman munafuka na ce, "Mamina me yasa kike yi yin haka?" Na faɗa kaman zan yi kuka. Mami kallona tayi ta ce, "Me nayi Banafshan Mami?" Gyara kwanciya nayi a cinyan Mamina na ce, "Dan Allah ki yi haƙuri Mami idan abinda zan faɗa zai ɓata miki rai, gaskiya ce komin ɗacinta faɗansa yana da kyau, Mami me ya sa za ki ce ba aure a gabanki? Mami me yasa kike nunawa mahaliccinki ba za ki cika sunnan ma'aikinsa Annabi SAW ba, Mami duk mace ko namiji da suka kai aure suka mutu ba aure fa Allah ma tausayinsu yake, Mamina nasan kin sani aure ni'ima ne kuma rahama ne, Mami Allah ya azurtaki da farinjini wanda wasu ma sai sun nema da kuɗi sun saɓa ma Allah sannan suke samu, Mami har yanzu taurarinki suna haskawa ba su disashe ba, me yasa ba za ki yi aure ba tun yana binki, kamun ya zo yana guje miki kina bin sa, Mami a haka akwai mai aure na ban da uba ina ƴar mace? Mami...." Maganan baki nane ya maƙale sakamakon wani irin stawan da Mamina ta daka mini, wanda ya sa na miƙe zaune babu shiri a rikice. "Banafshaaaa!!!!" Haka Mamina ta ƙira sunana a stawa ce. Tura baki nayi tare da runste ido na inma duka na Mami za tayi sai dai ta kashe ni, amma sai na faɗa mata gaskiya, ci-gaba nayi da magana ba ruwana da hucin da Mamina take yi, cewa nayi, "Mami ranan Alhaji ya ce miki Amaryansa kika ɓata rai, ya ce za ki haifa mini ƙanne kika yi fushi, Mami yau ina ji Abbaanmu ya ce zai aure ki nan ma kika ce ke ba aure bane a gabanki, Mami menene damuwanki dan Allah? Mami ya kike so a miki, duk da Alhaji mutum ne da yake rayuwan da bai dace da ke ba amma ya nuna yana ƙaunanki a haka, kuma zai aure ki, akwai soyayyan da ta fi wannan? Abbaa ya san ki shekara da shekaru, ya san duk abinda kike da wanda kike aikatawa na ba dai-dai ba amma hakan bai dame sa ba, bai hana sa ƙaunanki ba, yana sonki ya danne zuciyarsa, yanzu ya kasa haƙuri kuma ya furta miki kin ce ba haka ba ya kike so Mami? Wani irin masoyi kike son samu sai ki kawo maganan aure a starinki? Mami kina tuna mutuwa kuwa? Kina tuna za mu mutu ba tare da mun san yanzu ne ko anjuma ko kuma yaushe ba? Mami ita fa mutuwa ba ta alert a ko wane yanayi za ta ɗauke ka idan lokacinka yayi, Mamina kowa burinsa da fatansa ƙarshensa ya fi farkonsa kyau ya kuma gama da duniya lafiya yana mai imani mumini amintacce, Mami ke me yasa bakya fatan hakan? Mami dan Allah ki yi aure, wallahi idan ba za ki yi aure ba to kibar cewa aurar da ni ne damuwanki kuma burinki, sabida babu mai aure na a wajan mace, kuma ko akwai ma to ba auran zan yi ba, ba zan jure a goranta mini ina gidan mahaifiyata a ƙira ni da ƴar karuwa, sannan a ce nayi aure a goranta mini a ƙira ni da ƴar mace ba, Mami kina da dangi, kuma nasan ina da uba tunda mutum ba ya haifan yaro shi ɗaya, amma duk kin rabamu da su kin guje su kin wastar da su saboda me Mami? Ni Ko da mahaifina na raye ko ba ya raye ai ya kamata ki haɗa ni da danginsa saboda su ne gata na, kuma su za su shiga tsakanina da masu yi mini gori, Mami wallahi ko shegiya kika haife ni to haɗa ni da mahaifina ya fi wannan hukuncin naki kamata, kuma ni na yafe muku ina ƙaunarki a haka ke da mahaifi na, in ma ba ta hanyan da ya dace kuka same ni ba, na ɗauki ƙaddarata ta zamowa ƴar shege.........." Tasss!!Tasss!Tasss!!!!, Shi kawai kake ji Mami ta kwashe Banafsha da wasu mahaukatan maruka, idanuwan Mami jajazir kaman garwashin wuta ta ce, "Banafsha ni kike wastawa wannan kalaman? Banafsha har ni za ki saka a gaba kina mini magana kaman ƴar cikinki? To wallahi kin ji na rantse ranki zai yi mugun ɓacuwa akan rashin kunyan da kike mini, har kina ƙiran kanki shegiya kina faɗa mini kenan me nayi na haifeki? Banafsha...." Maganan bakin Mami ne ya sarƙe sai ga hawaye a idanuwanta, saurin juyawa tayi dan kar Banafsha ta gani, abinda bata sani ba kuwa duk da yanayin da nake ciki naga zubowan hawayenta. Mami juyawa tayi tana ƙoƙarin danne hawayenta amma ina sun ƙi stayawa, ɗakinta ta shige kawai ta kulle, kan gado Mami ta faɗa tare da sakin sabon kuka tana jin duk abinda ya faru shekaru ishirin baya yana dawo mata sabo dall kaman yau abin ya faru, cikin kuka ta ce, "Duk wanda ya aikata wannan mummunan tabo gareni in har da son ransa ban yafe masa ba duniya da lahira, in kuma shi ma bai yi da niya ba na yafe masa, amma duk mai hannu a faruwan wannan mummunan ƙaddara gare ni Allah zai saka mini, ban yafe ba, ban yafe ba, ban yafe ma ko waye ne ba, astagfirullah Ya Rabbi!..." Haka Mami ta dinga sumbatu tana kuka, saboda duk maganan da Banafsha take faɗa mata baya damunta sosai, amma maganganun yau ya soketa sosai, ya tuna mata da abinda bata son tunawa a rayuwanta, ya tuna mata da lissafin da ta jima da cire shi a rayuwanta, ta stani baya bata son tuna baya domin bata ji daɗin baya ba, haka Mami ta dinga kuka har sai da kanta ya fara mata mugun ciwo. Banafsha kuwa Mami na barin wajan ita ma ta ɓarke da nata kukan mai cin rai, ga ciwo a zuciyanta ga ciwon mara, ita ji take ma ta Mami ta bugeta har ta kasheta da ya fi mata daɗi, ko kaɗan bata ji zafi ko raɗaɗin marukan da Mami ta mata ba, kuka take kaman ranta zai fita, gaskiya ce ta faɗa wa mahaifiyarta, amma kuma ba wai dan ta sanya ta a damuwa ta saka ta zubar da hawayenta ba, lallaɓawa Banafsha tayi a dudduƙe ta ja jikinta ta ƙarisa ƙofan ɗakin Mami, tana turawa ta ji a kulle, a hankali da muryan kuka ta ce, "ki yi haƙuri Mamina, Allah ya huci zuciyanki, ba niya na saka ki a damuwa ba, niyana tunatar da ke da kuma baki shawara a mastayina na ƴar ki, Mami auren Abbaa Insha Allah alkairi ne gare ki Mamina, ki yi haƙuri ki auri Abbaa, shi cikakken me ƙaunaki ne Mami, wallahi ni nasan Abbaa zai fi Alhaji riƙe ki da amana, ki yi haƙuri Mami." Mami bata yi niyan yin magana ba, amma jin abinda Banafsha ke faɗa sai wani abun ya ƙara tokareta, stawa ta daka mata ta ce, "Banafshaaa! Ki ɓace mini a ƙofa kamun na fito na saɓa miki, shashashan yarinya wacce bata gudun ɓacin ran mahaifiyarta, duk haƙurin da nake akan rashin kunyan da kike mini, ke burinki kawai ki sa na miki baki ko? To ki cigaba kada ki dena zan miki bakin da kike so na miki, ɓace ki bani waje." Na buɗe baki zan bai wa Mami haƙuri, ta kuma sake mini wani gigitaccen stawan da ya saka ni barin ƙofan ɗakinta ban shirya ba, marana mugun murɗa mini yake ga kukan da nayi, tuni zazzaɓi yake son mini mugun kamu. Umaima bayan ta je tahfiz an tashi, Malam Abbo ya ƙara ba da saƙon gaisuwa zuwa ga masoyiyarsa Banafsha, Umaima ko da ta dawo bata shiga gidansu ba sai ta yi hanyan gidan su Banafsha, kuma dai-dai lokacin Umma ta fito a gida kenan, wani irin mugun kallo Umma ta bi Umaima da shi, tuni Umaima ta sha jinin jikinta tare da fara yarfe hannu dan tasan yau sai dai ɗan buzunta, Umma fasa fita tayi ta juya cikin gida, Umaima haka ta bi bayan Umma tana faɗin, "Ƙulya ƙulle bakin Ummana". Ummu tana zaune a palour, tunda ta ga yanda Umma ta shigo sai ta girgiza kai kawai dan bata san me kuma ya faru ba, Umma dakinta ta shige tana ƙwafa dan yau ba mai hanata daka Umaima sai ikon Allah. Umaima haka ta shigo tana raɓe-raɓe kaman wacce ta yiwa sarki sata, Ummu tana ganin Umaima tasan to da wani abun, kamun Ummu ta buɗe baki Umaima ta ce, "Ummu ki bawa Umma haƙuri kada ta dake ni, wallahi saƙo na je kai mata malaminmu ne ya aike ni wajanta." Ummu da ba ta gane ba ta ce, "Wajan waye kuma aka aike ki, kin dawo makaranta ba za ki taho gida ba, ina kika bi har Ummanki ta haɗu da ke a can." Umaima kaman za ta yi kuka ta ce, "Ummu wallahi ba inda na je, gidan su Banafsha ne kawai, kuma ban shiga ba da naga Umma." Ummu shiru tayi kawai ta rasa me za ta ce, dan tasan muddim Umma za ta daki yaranta, to bata isa ta ce ƙala ba, in ma ta saka baki to yanzu kuma faɗan zai dawo kanta. Umaima ta yi rau-rau da ido ta ce, "Dan Allah ki bata haƙuri Ummu." Ummu ta buɗe baki za ta yi magana sai suka jiyo muryan Umma tana faɗin, "Dan ubanki, kin staya a wajan uwarki ta biyu ko ba za ki zo ba ina jiranki." Umaima baya-baya ta fara za ta juya, sai Ummu ta girgiza mata kai ta ce, "a'a kar ki gudu Umaima, kije ki bata haƙuri, babban budurwa da ke Ummanki ba za ta dake ki ba, faɗa za ta miki kuma ko me ta ce ki bata haƙuri, ki ce kin ji kin daina." Umaima ɗaga kai tayi tana tafiya a hankali kaman wanda ƙwai ya fashewa a jiki, har ta shiga ɗakin Umma da sallamanta, Umma kuwa ko amsawa bata yi ba ta miƙe ta saka wa ƙofanta sakata, mugun kallo ta jefawa Umaima ta ce, "Me na ce miki ranan? Wato sai dai na stine miki ki lalace nine da asara ba uwar kowa ba ko? To kuwa ko ban stine miki ba zan daka ki sai na sauya miki kamanni, idan tare aka haifo ku da ita za ki faɗa mini yau." Umaima ta buɗe baki za ta bawa Umma haƙuri, amma ina sai sauƙan bulala ta ji a jikinta ko ta ina, Umaima na ihu, Umma na dukanta kaman an aiko ta bata fasa ba. Ummu na zaune a palour, tana jin ihun Umaima ta taho da sauri duk da bata shiga ɗakin Umma, amma ta tura ƙofan da niyan shiga, sai ta ji da gam a garƙame da sakata, magana take tana faɗin, "Dan Allah dan Annabi SAW ki ƙyaleta ki yi haƙuri Maman Kabeer, ki bar dukanta haka nan...." Magiya Ummu ta dinga yi amma Umma ko jin ta bata yi ba, balle ma ta saurareta kawai jibgan Umaima take yi. Umaima tun tana kuka da ƙarfi har ta zube a waje guda muryanta ya dishe, ba abinda take faɗi sai, "ki yafe ni Umma, ki yi haƙuri ba zan ƙara ba, wallahi Abbaa ne ya ce muje, ki yi haƙuri Umma ki mini rai, zan mutu, wayyoooo! Ummuna!!!" Umaima na faɗan haka ta sume. Umma duk da Umaima ta sume amma dukanta take zuciyanta kaman zai faso ƙirjinta ya fito, magana take kaman zararriya, "Ni za ki mayar ƴar iska bansan me nake yi ba, wato kin faɗawa ubanki sai ya saka ki gaba kuka je, ban isa da ke ba, to gwanda ma na kashe ki na huta da ki kasheni da naki takaicin, har da ke ubanki zai je zance, duk munafurcinku ne ya ja in ba haka ba, me za'a yi da karuwa a kishiya, ai sai ta addabi kowa ta ishi kowa ta nemi ɗaga mutum akan yaransa..." Umma tana magana tana dukan Umaima tana haƙi, har sai da ta ji kaman za ta sume ita ɗin ma, sannan ta jefar da bulalan ta jawo ruwa ta kwankwaɗa ta wastawa Umaima, wani wawan ajiyan zuciya Umaima ta sauƙe tare da sakin marayan kuka tana numfashi a hankali-hankali. Ummu kuwa da ta gaji da magiyan, ficewa tayi ko ta duba samarin gidan amma ba kowa, Abbaa ma bai dawo ba, haka ta dawo cikin gidan lokacin Umma ta gama jibgan Umaima, Ummu kaman za ta yi kuka haka ta koma ƙofan ɗakin Umma, amma har lokacin bata buɗe ƙofan ba, ƙarshe Ummu ɗakinta ta koma. Umaima na zube a wajan, Umma ko ta kanta bata bi ba, ta shige bayi ta wasta ruwa, ƙwafa tayi tare da kallon Umaima ta ce, "tashi ki fice mini a ɗaki, idan kin so gobe na hanaki yin abu ki yi, idan yayanki ya dawo kuma na faɗa masa ya ƙara miki, kinsan dukansa kuma sarai." Umaima ko yastanta ta mosta raɗaɗi take ji, dan ta daku sosai ba ƙarya, Umma tsawa ta mata, dan dole Umaima ta ja jikinta tana kuka ta shige ɗakinsu, ga shi Ummu bata san ta fito a ɗakin Umma ba, haka ta zube a stakar ɗakinsu tana kuka har baccin wahala yayi gaba da ita. Ummu kuwa tana ɗakinta, bata san Umaima ta fito ba, har Abbaa ya dawo a palourn sa na cikin gida ya gama komai ya tafi wajan Mami, har ya dawo duk bai san wainar da ake toyawa ba a cikin gidan, sai da ya shigo ciki ya ji gidan shiru kaman ba kowa, ɗakin Umma ya fara shiga sai ya sameta tana sallah, juyawa yayi ɗakin Ummu, samunta yayi ta haɗa hannayenta ta tallafe kuncinta, Abba ƙarisawa yayi wajanta ya zauna tare da cire mata tagumin da ta yi, Ummu ɗagowa tayi ta kalli Abba sai kawai ta faɗa jikinsa tana faɗin, "Dan Allah kabar maganan auren Mamin Banafsha, ka yi haƙuri, kuma ka ce Umaima ta bar shiga gidan, komai ya wuce, zaman lafiya ya fi zama ɗan Sarki." Abbaa kallonta yayi ya ce, "Me ya faru? Me yasa kika ce haka? Bayan ke kika kawo shawaran kuma na amsa, meyasa?" Ummu kaman za ta yi kuka ta ce, "nidai dan Allah ka bari, nasan ni na bada shawara amma kuskure nayi, dan Allah ka mance da batun ka ji Alhaji." Abbaa miƙewa yayi ya ce, "Ba zan zamo mutumin banza ko kuwa mijin da ake juyasa ba, ke kika yi magana ba ni na ce ba, dan haka bakin alƙalami ya riga da ya bushe, na samu Ramla na faɗa mata abinda ake ciki, yanzu haka amsanta nake jira, kuma ina da tabbacin amsan nata eh ne" yana gama faɗa ya nufi hanyan waje fiska ba sassauci, ta ya za ta ce abu kuma yanzu ta ce a'a idan ba ta renasa ba, to shi ya riga da ya sakawa zuciyansa son Mamin Faɗima, kuma idan har bai aureta ba Allah ne kawai bai nufa ba. Ummu jiki a sanyaye ta ce, "ka yi haƙuri Abbaansu ba nufi na kishi nake yi ba, duk da nasan kishi dole na yi sa tunda ina ƙaunanka, amma ba hakan bane dalilin maganana, ka je ɗakin Maman Kabeer ka duba halin da Umaima ke ciki, na tabbata kai ma za ka fahimci janye maganan nan shi ne alkairi da zaman lafiya." Abbaa bai kuma cewa da Ummu komai ba ya fice a ɗakin, ɗakin Umma ya koma lokacin ta idar da sallah, ba murmushi ba komai kaman an mata dole ta ce, "Sannu da dawowa." Abbaa ko ta sannunta baya yi ya ce, "Ina Umaima?" Umma taɓe baki tayi ta ce, "tana ɗakin su." Abbaa bai ce komai ba ya juya, da sallama ya shiga ɗakin su Umaima, bai ma kula da ita a stakar ɗakin ba, sai da ya ga bata kan gadonsu sannan idanuwansa ya sauƙa a stakar ɗakin, da mugun sauri Abbaa ya nufe ta a rikice yana faɗin, "Ummu-khultum lafiya?" Umaima ta jima da tashuwa daga baccin wahala, amma zuwa lokacin jikinta yayi stananin stami, ba abinda take sai aikin nishi, ko da taji Abbaa na ƙiran sunanta ba daman amsawa, sai kuka ta sanya wanda idan ba kana kallonta ba, ba za ka ji sautin kukan ba saboda yanda muryanta ya dishe. Abba yana taɓa jikinta yaji yayi zafi sosai, ya juyo da ita kuwa ya ga fiskan a kumbure alaman ta sha kuka, kallonta yayi cikin damuwa ya ce, "Me ke damunki Umaiman Abbaa?" A hankali take mosta laɓɓanta tana jan zuciya ta ce, "Umma ceeeee" ta ƙarishe maganan kaman za ta sume. Abbaa ficewa yayi ya nufi ɗakin Umma, amma ya samu ta kulle ƙofa, bugawa yayi taƙi buɗewa, ɗakin Ummu ya koma ya ƙirata, tana shigowa ta kalli Umaima sai ta fara hawaye tana mata sannu, Umaima lumshe ido tayi cikin azaban da jikinta ke mata, Abbaa ya ce, "Khultum shiryata mu tafi asibiti" yana faɗa ya fice. Ummu haka ta ƙoƙarta ta ɗaga Umaima ta ja ta banɗakinsu da ke cikin ɗaki, ruwan zafi ta koma ta ɗauko a ɗakinta ta zo ta haɗa ruwa, kamawa Umaima jikinta tayi, ta mata wanka ta shiryata sannan ta yiwa Abbaa magana akan ta gama. Abbaa da kansa ya ɗauki Umaima suka fice a gidan, asibiti ya kai ta a cikin gari, sai dai an kama su a gado, dole Ummu ta kwana a asibiti, shi kuma Abbaa ya koma gida, bai bi ta kan Umma ba dan tabbas zai yi abinda ba dai-dai ba, mataki ne kuma ya ɗauka, in Allah ya yarda zai auri Mamin Faɗima ya ga ta ƙarshen rashin mutuncin ta. Ɓangaren Mami da Banafsha haka suka kwana, ba wanda ya fito balle ya sa wani abu a cikinsa, Mami sai da dare tayi sosai sannan ta fito ta zo ɗakin Banafsha, samu tayi tana bacci jikinta da zafi, kayan jikinta ta rage mata ta share mata jiki da towel mai sanyi, sannan ta tofa mata addu'a ta ja mata ƙofa ta koma nata ɗakin, alwala Mami ta ɗaura ta dinga sallah, har sai da ta ji ƙiran assalatu, bayan tayi sallahn asuba tayi ayyukanta ta gyara gidan staff, ɗakin Banafsha ta shiga ta sameta ta fito wanka kenan, Mami murmushi ta sakar wa Banafsha ta ce, "shalelen Mami har an tashi, fatan jikin da sauƙi?" Banafsha wani abu ne ya soki zuciyanta, sai take jin sam-sam bata kyauta ba duk da gaskiya ce, amma Mami bata chanchanci haka daga gare ta ba, hugging na Mami ta yi ta amsa da sauƙi, ta gaisheta ta amsa, Banafsha ta ce, "ki yi haƙuri Mamina." Murmushi Mami tayi ta ce, "ya wuce Allah miki albarka, Allah shirya mini ke." "Ameen Mamina" na amsa ina murmushi, haka na gama shiri muka fice da Mami muka karya, yau ma ba iya zuwa makaranta zan yi ba Mami ta ce na bari sai wani Monday kawai, muka zauna muna hira Mami na ƙara mini faɗa. Haka rayuwa ta dinga tafiya har aka cinye wannan sati Banafsha bata je makaranta ba, kuma sai da ta cika kwana bakwai ciff sannan ta samu sauƙi ranan Lahadi, Umaima ma duk sauran kwanakin bata je makaranta ba, kwanan su kusan huɗu a asibiti sannan aka sallamesu, har Ya Mus'ab ya zo shi ma daga Camaroon duba jikin Umaima, Ya Kabeer su ya Sadeeq su ya Farooq duka, kowa duk ya ji abinda Umma ta yi amma ba daman magana sai ido, Abbaa ma idon ya zuba dan shi ya gama ɗaukan nasa matakin, Ummu kuwa bata da bakin magana tunda gori Umma ke mata ko ta yi magana ta ce ai ba ƴar ta ba ce, haka ta dinga jinyan Umaima har ta warke, ya Danish ne kawai bai zo ba kwata-kwata ga shi har weekend ya ƙare yau Lahadi. Ɓangaren Malam Abbo kuwa ganin Umaima ma ta daina zuwa makaranta kwana biyu ba ya jin halin da masoyiyarsa ke ciki, tuni hankalinsa ya tashi, haka a daddafe ya daure har sati ya cika, ranan Lahadi da yamma ya sha wankansa ya chakare ya shirya rass ya nufi gidan su Banafsha, farinciki kawai yake ciki da ɗauki gani yake ba ya isa da wuri saboda yanda yake ɗaukin son ganin abar ƙaunarsa, Sayyadarsa, Malama Faɗima. ⭐ Bunayd hutawa yayi sosai ba wanda ya san yana sashinsa a gidan, sai da General ya ƙirasa a waya sannan ya faɗa masa ai yana cikin gida ma tun da ya dawo ya taho gidan, General mayar da wuƙan yayi ya kashe wayan yana sakawa Man nasa albarka. General layin Suhail ya kuma ƙira yana ɗauka ya rufe shi da faɗa ya ce, "Suhail ina ce dai ba gidan ubanka ba ne a Turkish ɗin nan ko? To idan ka kuskura gobe ba ka dawo ba sai na ƙwace har jarin da yayan naka ya baka, sai naga ta inda za ka zauna a ƙasar mutane babu kuɗi." Suhail murmushi yayi da haɗaɗfiyar muryansa ya ce, "sorry General! Na gama shirin komai jirginmu da asuba zai tashi." Ƙwafa General yayi ya ce, "Idan ma baka dawo ba kasan abinda zan iya yi, dama har yanzu ban huce da ƙin aikin soja da ka yi ba, kuma ka zo kana zuga mini yarona Nabeel." Suhail dariya yayi ya ce, "Ni kuma ka yafe ni ne General? Ko da yake ni da nake da yaya CAS Bunayd ko General ya yafeni normal ne, daman ni yaya ne babana." General murmushi yayi ya ce, "Za ka dawo ka same ni, daman shi yake ɗaure muku wajan zama." General haka yake da yaransa maza kaman abokanayensa, musamman CAS Bunayd, kwata-kwata General ba shi da zafi, kuma haka matar sa Hajiya Huraira. Momsee da ke zaune a gefe dariya tayi ta ce, "Dear gaskiya yarannan su maida ka kaka." General kansa ya shafa ya ce, "Alhamdulillahi kawai za mu ce, yara arziƙi ne tunda Allah ya bamu, dole mu jawo su jiki dan mu ji daɗin nuna musu dai-dai da ba dai-dai ba, yiwa yara zafi bai da wani fa'ida, illa ya saka yaro ba zai sake da kai ba balle kasan damuwansa, ko yayi shawara da kai, Allah dai ya musu albarka ya kare su a duk inda suke." Da, "Ameen" Momsee ta amsa, suka cigaba da hiransu. Bunayd yau daurewa yayi bai je ko ina ba, ba dan yaso ba sai dan General bai cika son yawan fitansa da dare sosai ba, idan ba kamawa tayi ba, amma idan ba saboda General ba sam-sam Bunayd baya son zama, shi zuwa wajan chasu a jininsa yake, ko da ba zai yi komai ba sai dai ya bawa idonsa abinci yayi catching fun's, sai da ya gama hutawansa sannan ya shigo palourn nasu na ƙasa, su Suhaila suna ganinsa suka fara washe baki, shi kuma haɗe fiska yayi dan ya san ba zai wuce su ce yawo da daren nan ba, fiska ba Rahama ya ce, "Ku kawo ƙur'anan ku." Stuttt! Duk suka miƙe suka je suka ɗauko, General da isowansa palourn kenan murmushi yayi ya ce, "Kaman haɗa fiskan da gaske ne, ai ina ga yaran nan sun gama lashe maka zuciya, musamman Suhaila da Nabeela." Bunayd shafa kiston kansa yayi bai ce komai ba, ya fara sauraran karatun ƙannensa sai ga Nabeel ya shigo, kallo ɗaya Bunayd ya masa tuni ya gane nufinsa, shi ma ɗauko nasa ƙur'anin yayi da littafin da suke yi na addini, Bunayd sai da ya duba karatun ƙannensa duka ya musu ƙari, sannan ya kuma suka zauna hira ana raha, bai cika magana sosai ba amma idan da ƙannensa ne kuma yana mood to duk shirmen su yana biye musu. Da dare ya ja sosai sai General ya kora su kowa ya kwanta, da safe a fara shiri sai Kano in Allah ya yarda. Bunayd yana komawa sashinsa sai ga ƙira, ganin mai ƙiran sai ya taɓe baki, a fili ya ce, "Yoruba people akwai reni, to nima ba zan yi attending naka ba sai gobe." Yana gama mitansa ya kashe wayansa ya kwanta. Cikin dare ya tashi yayi nafilfiulunsa yanda ya saba, sannan ya koma ya kwanta. Washe-gari Suhail da wuri ya iso, lokacin kuma kowa ya gama shiryawa, ba jimawa suka kamo hanyan Kano amma ta Flight, jirginsu na sauƙa motoci uku suka zo ɗaukansu daga gidan Alhaji. Shigan su Bunayd gidan yayi dai-dai da shigowan motan Hajiya Sa'adatu da sai yau ta dawo daga inda ta je, su Suhaila duk da ba wani sake musu Hajiya Sa'adatu ke yi ba amma duk sun yi hugging nata, a yastine ta amsa, General da Momsee duk sai su suka ɗaga mata gaisuwa, sannan ta amsa a gadarance, da yake General ma da nasa part ɗin a gidan, sai suka wuce duka can, Majeeder tunda ta ji zuwansu ta fito ta rungume sister's nata mata, da kuma General da Momsee, tunda ta maƙale wa Bunayd ko mostawa zai yi tana riƙe da shi, ba ƙarya Bunayd ma yayi mugun kewan ƙanwar tasa dan ya kwana biyu bai zo ba. Alhaji da kansa ya saka masu aiki suka kai wa su General abinci, sannan da waɗanda za su musu aiki har su koma. Hajiya Sa'adatu tunda ta shige ko leƙowa bata kuma yi ba, sai kawai cin magani take yi kaman ba ɗan uwan mijinta da yaransa ba ne suka zo, kaman wasu bare daban. SU WAYE WANNAN AHALI? MENENE FARKON LABARINSU? waiwaye adon tafiya, Inshà Allah a next page za mu ji taƙaitaccen tarihin wannan ahali. Not edited again, ayi haƙuri da typing errors, Uwar batoorl jikin sai a hankali. Masu Sharhi ina matuƙar Godiya 👏 Uwar batoorl taku. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Hafsat Umar Ɓingel kabi Masoyiya bealkysou Habiba muhammad Yusuf Ameera اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 61 _ 65 ALHAJI SULAIMAN ILYASU KWALLI! Shi ne kakan Bunayd, Sulaiman kwalli wanda aka fi ƙira da Sule kwalli shi asalin ɗan jihar Sokoto ne, a ƙaramar hukumar Binji, su biyu iyayensu suka haifa shi da ƙanwarsa mai suna Rahama, Sule da Rahama sun taso cikin gata da soyayyar iyayensu, saboda iyayensu na da rufin asiri Masha Allah, su Hausa-Fulani ne, bayan kiwon dabbobi da mahaifinsu Ilyasu ke yi har da sana'ar hannu yana yi wacce ta danganci nau'in su kwalli, Sule da Rahama duk iyayensu sun saka su a makaranta ta muhammadiya da kuma ta ilimin zamani(boko), lokacin da Sule yayi nisa a karatu sai shi ma ya ɗau sawun babansu Ilyasu kwalli ya fara sana'a irin tasa, cikin ƙanƙanin lokaci da ikon Allah shi ma ya staya da ƙafansa, a lokacin ne kuma ya samu mata mai suna Hauwa'u ƴar gidan wani babban mutum ɗan siyasa a cikin birnin Sokoto. Bayan neman da suka yi na ɗan lokaci sai aka yi auransu, bayan biki ba jimawa Sule kwalli ya samu haɗaɗɗen gidansa a cikin birnin Sokoto, nan ya nemi da su koma duka da iyayensa amma sai iyayensa suka ƙi su sun fi son zaman Binji, haka Sule ya tattara da Amaryarsa Hauwa'u suka koma cikin birnin Sokoto da zama, sai dai sa'i zuwa lokaci su dinga kai wa iyayensa ziyara, Hauwa'u matar Sule bafulatana ce gaba da baya, kuma kyakkyawa ce ta ƙarshe ma, dan haka suna zaune lafiya da mijinta, a sanda auransu ya cika shekara a lokacin ne kuma ta haihu ɗan ta namiji santale mai matuƙar kama da mahaifinsa Sule, ranar da ya cika kwana bakwai yaro ya ci sunansa Mukhtar, kuma a wannan lokacin Rahama ƙanwar Sule ta dawo gaban Sule da zama tana kan karatunta, saboda akwai ratan shekaru sosai stakaninta da yayan nata. Mukhtar na da shekaru biyar a duniya sai Hauwa'u ta kuma haihuwan yaronta kyakkyawan gaske namiji mai matuƙar kama da ita, kaman kakinsa ta yi, ranan bakwai yaro ya ci sunansa Sufyan, zuwa wannan lokaci Ilyasu ya manyanta sosai kuma matarsa Salamatu na fama da cutan ajali, shi kuwa Sule ya zama mai kuɗin gaske, kullum sintirin asibitin neman magani suke da mahaifiyarsa amma kwana ya riga da ya ƙare babu dabara, haka saƙon mutuwanta ya riske su, a ranan suka tattara suka tafi Binji, bayan an yi bakwai suka tattaro suka dawo, sai da aka yi arba'in sannan Ilyasu ya yarda ya dawo gidan Sule da zama. Bayan wasu shekaru biyar Hauwa'u ta kuma haifan yaranta ƴan biyu mata, aka sakawa ɗaya sunan kakansu da ta rasu, Salma ɗayan kuma Salima, bayan haihuwansu ba jimawa Rahama ta samu mijinta dan ita kam auren ya ɗan mata jinkiri ma, shekaranta biyu da aure ta haihu ƴar ta mace ranan suna ta ci sunanta Huraira, kuma a lokacin Hauwa'u ta ƙara haihuwan ɗa namiji mai suna muhammad, amma ita rahama tun da ta haihu ciwon ciki ke damunta, a ranan da suka yi kwana ishirin da haihuwa a ranan ta cika. Rasuwan Rahama sosai ya taɓa ahalinta, musamman da ta bar jaririyan da ko wata bata yi ba a duniya, mijin Rahama ya bar Huraira a hannun kawunta Sule saboda kara, Hauwa'u ta nemi ta haɗa su ta shayar tare da muhammad amma Ilyasu ya hana, dan haka madara ake bata, tun su Huraira ba su shekara ba muhammad yaron Hauwa'u ya koma, a wannan lokaci kuwa Mukhtar da ƙaninsa Sufyan sun zama Samari dan Mukhtar yana da shekaru kusan goma sha bakwai, shi kuma Sufyan shekaru sha biyu garesa, twin's kuma shekarunsu bakwai kuma duk suna nan lafiya-lafiya, Mukhtar ma yana karatu kuma yana kula da harkoki irin na mahaifinsa Sule kwalli, yayinda Sufyan ya dage shi Soja zai yi, kuma da yake ba rayuwan yau ba ne sai ya samu cikin ikon Allah. Lokacin da Huraira ta yi shekaru biyar a duniya, lokacin Ilyasu ya buƙaci da su kai ziyara a Binji wa sauran ƴan uwa, Mukhtar da Sufyan duk suna makaranta ba sa gida, dan haka sai duk suka shirya da Sule da matarsa Hauwa'u da Ilyasu babansa da yaransa ƴan biyu, Salma da Salima da kuma Huraira, sun shirya sun kama hanya, lafiya-lafiya haka suka isa, suka zaga dangi suka musu alheri, kwanansu biyu suka tattaro dan su dawo gida, a hanya kuma suka haɗu da ƴan fashi, duk da sun samu abinda suke nema amma ba su bar kowa da rai ba haka suka kashe su suka yi gaba, labari na iske Mukhtar da Sufyan kaman za su yi hauka haka suka zo, sai dai wajan yi wa gawa sutura aka samu Huraira da ranta, storita da lamarin da ya faru ne ta yi dogon suma ba wai kasheta aka yi ba ita. Wannan rashi kaman zai haukata Mukhtar da Sufyan, sannan Sufyan ya ɗau alwashin kama masu laifin sai ya ɗau fansan iyayensa da ƙannensa, Mukhtar kuwa sai dai ido kawai, Huraira haka ta zama shiru-shiru ita ma kaman mara ishashshen lafiyan ƙwaƙwalwa. Malam Zahraddin mahaifin Huraira shi ya riƙe su Mukhtar tunda da girmansu ba buƙatan sai ya riƙe musu dukiya, kawai ya riƙe su ya zama kaman mahaifinsu ne dan saka halaccin iyayensu a garesa na riƙe masa ta shi yarinyar da kuma basa mata. Shekaru sun ja, Mukhtar ya zama Alhaji kuma cikin ikon Allah tunda al'amuransa suka yawaita a Kano sai ya tattara su suka koma can, a Kano kuma ya samu matan aure Sa'adatu ƴar gidan wani kansila, tun da Alhaji Mukhtar yayi aure aka tura Sufyan aiki a Abuja, ita kuwa Sa'adatu wulaƙanci ne da ita ba kaɗan ba, haka ta ke yi wa Huraira da mahaifinta, Alhaji ya stawatar sosai, amma sai mahaifin Huraira ya ce za su je Sokoto ganin gida, duk saboda kada yana babba ya haddasa rashin zaman lafiya stakaninsa yaransa, haka ya tattara Huraira suka koma Sokoto a can kuma ta cigaba da karatu cikin kewan yayunta dan sosai Huraira ta saba da su Mukhtar. Sufyan daga Abuja aka kuma shillasa Lagos, kuma tunda ya je Lagos ta masa daɗi ya zauna daram abinsa, ba batun aure a lissafinsa, sai dai ya kawo wa yayansa ziyara kwana ɗaya biyu ya koma, ya je Sokoto shi ma kwana ɗaya biyu ya koma Lagos, yana aikin Soja kuma yana da business wanda ya ɗaura masu kula masa da business ɗin, kuma a ɓangaren aikinsa ko da yaushe cikin ƙarin girma yake, inda yanzu yake mastayin General, kuma cikin ikon Allah da taimakon bincike, ya samu ya kama waɗanda suka kashe masa iyaye, hukuma ta yanke musu hukunci, saboda sun ishi al'umma daman. Hajiya Sa'adatu ta haihu ɗan ta namiji mai shegen kyau mai kama da Sufyan kaman shi yayi kakinsa, idan ka ga yaron za ka ɗauka ɗan larabawa ne, yaro ya ci sunansa muhammad Bunayd, Sa'adatu ta ce ta daina haihuwa ita ba za ta iya ba ta stofe da wuri, ita ba son haihuwa take ba, kuma ko shayar da Bunayd bata yi sai Alhaji ya stawatar mata, amma duk da haka sam-sam Alhaji bai rageta da komai ba, domin da mahaifinta ya rasu aka raba gado aka bata nata, sai ya ƙara mata jari a kai ta fara business, wanda cikin ƙankanin lokaci kasuwancinta ya bunƙasa ta zama Hajiya ita ma, sai dai wulaƙanci ya ƙaru, kwata-kwata Hajiya Sa'adatu bata son kowa ya raɓe ta ko mijinta, hatta Sufyan da yake ƙanin Alhaji Mukhtar to ba ta ƙaunarsa, komai ita ɗaya haka take so, ko Alhaji zai yi yaya da ita yanzu bata yarda ta je Sokoto, sai dai ta kawo masa uzurin ƙarya. Sufyan ya fi Alhaji Mukhtar ziyara sosai ba kaɗan ba, dan sai Sufyan ya je Sokoto sau biyar Alhaji Mukhtar bai wuce ya je sau biyu ko ɗaya ba, tunda Hajiya Sa'adatu ta haihu shikkenan kuma sintiri ya samu Sufyan Kano to Lagos, Allah ya ɗaurawa Sufyan stanstar ƙaunar Bunayd, dan ko da Bunayd yayi shekara biyu sai Sufyan ya ɗauke sa suka tafi Lagos, duk da ba shi da aure amma ya samu wata musulmar Yoruba tana kula masa da shi, kuma shi ma da kansa yana kula da Bunayd kaman shi ne mahaifiyarsa, kashinsa fistarinsa komai akan Bunayd ba abinda General Sufyan bai iya ba, kuma karatunsa Arabic da boko yana kula da shi, musamman abinda ya shafi Addini da kansa yake zama ya koya masa, baya taɓa yarda aiki ya sha kansa bai duba karatun Bunayd ba, gata kam iya gata Bunayd na samu a wajan General Sufyan, gatan da ko ɗan cikinsa ba lallai ya samu ba. Alhaji Mukhtar kuwa ba abinda ya ce dan General Sufyan ya ɗau Bunayd, saboda shi hakan ma hankalinsa ya fi kwanciya, akan hali irin na matarsa, ita Hajiya Sa'adatu kuwa gaba-ɗaya hankalinta na kan business nata ko a jikinta, sai hamdala ma da tayi an rage mata aiki, dan ita ko haihuwan bata so ba balle yaro ya takura mata, kwata-kwata Bunayd bai san wani daɗin mahaifiyarsa ba, shiyasa shi ma a duniyansa komai nasa General ne, dan da shi yayi mugun sabo. General Sufyan ko ina zai je ƙafansa ƙafan yaronsa Bunayd da ya zama kamar abokinsa, har Sokoto suke zuwa tare har wajan wani abokinsa Soja ɗan gidan wazirin Sarkin Sokoto, kuma Bunayd ya shaƙu da Huraira sosai, haka mahaifin Huraira ma sosai yake ƙaunar Bunayd, dan Bunayd yaro ne da duk wanda ya kallesa to sai ya shiga ransa, ba shi da ƙiriniya irin na sauran yara, kana ganinsa kaga zubin sadauki, yana da raha idan yayi niya musamman idan yana tare da General Sufyan ko Alhaji Mukhtar. Bunayd na da shekaru sha uku mugun soyayya ya ƙullu stakanin General Sufyan da yarinyar Sultan na Sokoto, ta sanadin abokin General Sufyan, Major Ahmad wanda yake yaro a wajan wazirin Sarkin Sokoto, soyayyan General Sufyan sosai yayi nisa shi da Gimbiya Ramlat, ta san yana da yaya kuma tasan yana da yaro, wani stautsayi ne ya faru stakaninsu wanda yayi sanadin raba soyayyansu, damuwan da General Sufyan ya shiga shi ya sanya mahaifin Huraira ya basa auren Huraira tunda ba ta haramta a gare sa ba، duk kuma abinda ke faruwa Alhaji Mukhtar bai da labari dan yayi tafiya ƙasar waje. Ba jimawa aka yi auren Huraira da General Sufyan, Bunayd sosai ya ji daɗin da Huraira ta dawo gidansu, kuma Huraira stakani da Allah take riƙe Bunayd da soyayya kaman ɗan cikinta, duk da ba wai ya cika zama bane, sakamakon makarantan sojojin sama da General ya saka shi, da farko Sojan ƙasa yayi niyan turasa amma sai Bunayd ya ce Air Force yake so, shi jirgi yake so. Alhaji Mukhtar ya dawo ya samu labarin abinda ya faru nan ya bi su da addu'an Allah ya kyauta, a wannan lokacin ne kuma ciki ya bayyana jikin Hajiya Sa'adatu ba shiri ba sanarwa, duk ta gama sakankancewa ta daina haihuwa tunda ta yi planning, amma ikon Allah sai ga ciki, baƙin ciki kaman ta yi yaya, ta yi iya yinta amma ta kasa ɓarar da cikin, haka ta haƙura ba dan ta so ba sai dan ba yanda ta iya da nufin Allah, ciki na kai wata tara ta haifa yarinyarta santaleliya kyakkyawa mai sunan mahaifiyar su Alhaji Mukhtar, Hauwa'u amma suna ƙiranta Majeeder. Huraira na cika shekara a gidan General Sufyan ta haifo yarinyarta mace kyakkyawa mai kama da Alhaji Mukhtar, yarinya ta ci suna Ramla, bayan shekara biyu ta kuma haihuwan ƴan biyu mace da namiji, Suhail da Suhaila, bayan wasu shekaru biyun ta kuma haihuwan ƴan biyu, Nabeel da Nabeela, bayan shekaru biyu ta haifi yaronta namiji amma ya koma, saboda wahalan da ta sha da cikin yaron sai General ya buƙaci da a stayar da haihuwan, Allah ya yiwa waɗanda suka haifa albarka. Hajiya Sa'adatu tun da ta haifi Majeeder sai ta je asibiti a ɓoye aka cire mata mahaifa ba tare da sanin Alhaji Mukhtar ba, kuma har yau bai sani ba. Yaran gidan General Sufyan sun taso cikin gata da soyayya na iyaye da kuma yayansu Bunayd, kaman yanda General ya kula da karatun Bunayd, haka shi ma yake kula da karatun ƙannensa, sosai yake ƙaunar ƙannensa, amma sam-sam ba ya shiri da Mom tasu Hajiya Sa'adatu. Bunayd ya fara abota da Abeed ne tun san da ya shiga makarantar sojojin ƙasa da farko, sai ya zamana duk da ya koma air force school to ba su bar abota ba, shi ma Abeed ɗan Kano ne, mahaifinsa babban ɗan kasuwa ne, haka mahaifiyarsa ma tana nata business ɗin. Malam Zahraddin mahaifin Huraira bai jima da rasuwa ba, sai bayan rasuwansa sannan suka ɗaga ƙafa da zuwa Sokoto. Alhaji Mukhtar business yake sosai, kuma ya mallaki companies da dama, a Nigeria da ma ƙetaren Nigeria, shi ma General yana da nasa business ɗin kuma shi babba ne a sojoji. Bunayd ma ba iya aikin Soja yake yi ba, domin daga General har Alhaji Mukhtar ba wanda bai ba sa jari ba, sannu a hankali ya fara business da kuɗaɗen, kuma shi da kansa yake kula da harkokinsa, sai dai kawai wakilai da yake da su, ya na da gidaje uku a cikin Lagos, sannan yana da gida a Kano, sai kuma ƙasashen waje da ya yawaita zuwa, duk inda business nasa ya yawaita a can yana da gida, ƙasashe shida duk ba inda bai da haɗaɗɗen gida a can, kuɗi CAS Bunayd yake da shi na fitan hankali wanda har ya ƙere iyayensa da suka basa jari, kuma shi ma duk ƙannensa maza ya basu jari duk da ƙananun shekarunsu, dan Suhaila shekarunsa 17 ne, amma shi ma yana da nasa Companyn a Turkish inda yake karatu, sannan yana zama a gidan Bunayd da ke can. Nabeel mai shekaru 14 yana cikin na 15, shi ma Bunayd ya mallaka masa nasa rabon, yanzu haka dai rikice yake da General, shi Nabeel ya ce baya son aikin Soja, General kuma ya ce sai yayi. Majeeder ta taso sai a hankali, amma da yake ita mace ce da sauƙi, Hajiya Sa'adatu na kula da ita ba kaman lokacin da ta haifi Bunayd ba, Alhaji ganin irin halin Hajiya sai shi da kansa ya ke duba duk abinda ya shafi Majeeder, tarbiyanta da komai nata, bai bari rashin kulawan mahaifiya ya sa yarinyarsa ta lalace ba, tana karatu boko da Arabic, bai jima ba da suka yi musabaƙa a cikin Kano kuma ta zo ta ɗaya, a boko kuwa tana matakin degree tana shekaranta na kusa da final year, inda take karantar Agriculture, a University na Kano. Ramla tana karatu a babban Private University na Lagos, Anchor university, inda take karantar Education and computer science, sai kuma Suhaila da take nursing school a Lagos ɗin tana karantar midwifery, ita Nabeela kuma yanzu ne za ta tafi matakin gaba da secondary, ta dage University na Abuja za ta je, Bunayd kuma ya ce ba za ta yi zaman hostel ba, dole ita ma a Anchor university za'a nema mata admission ta karanci accounting, Suhail dai yana Turkish yana karantan abinda ya shafi business, shi ka Nabeel ya ce business administration zai karanta ko a Lagos ko kuma wata ƙasan, amma sam General ya ƙi. Bunayd na da tarbiya dai-dai gwargwado dan sosai yake kula da abinda ya shafi addininsa, kuma yana da girmama manya, sai dai yana da abin dariya wani lokacin, kuma idan hali ya mosta to yana da miskilanci, bayan Abeed yana da wasu abokanan amma a wajan aiki, kawai ba wai ana together irin sosai ɗin nan ba ne kaman yanda yake da Abeed, kuma a wajan abokanansa ya koyi zuwa su club da sauransu, ba inda za'a je bai je ba amma kuma tunda ya ke bai taɓa kai abinda ya shafi giya ko kusa da bakinsa ba, kuma duk iya yanda sojoji ke harka da mata to shi babu shi a ciki, domin shi gani yake ko ashawo ba su gana waye wa ba, shi ya fi son ya samu wayayyiyar mace wacce bata da kunya ya aura, sam-sam baya son Ustaziyan mace, dan gani yake duk ustazan matan nan ba abinda suka sani sai ƙauyanci da kunya ba su iya soyayya ba, kwata-kwata bai taɓa yin ko budurwa ba a rayuwansa, duk da kuwa harin da mata ke kawo masa ta ko ina, ba ya wulaƙanta mace amma kuma yana koya mata tarbiya, dan idan mace ta dame sa da maganan banza sai ya koya mata hankali wai a kan me za ta taɓa sa bata biya sadaki ba, maganan iyayi kuwa akwai a bakin Bunayd sinƙi-sinƙi. Bunayd ɗan shashu ne sosai, indai zai je club to ko mazari ne a wajan ba zai kai sa rawa ba, kuma tun tashuwansa ya ke ƙiran General Sufyan da General, Alhaji Mukhtar kuma ya ce masa Sir, har sai da aka haifi ƙannensa suka fara ƙiran Alhaji da Papi sannan wani lokacin yakan ce wa Alhaji Papi, General kam duk da ana ce masa Affa, to sai ranan da ya ga dama zai faɗi hakan. Wannan shi ne asalin wannan tarihin wannan ahali a taƙaice, kowa kun ji halinsa saura kun ji a baya, sauran kuma za ku ji a gaba. CI-GABA LABARI Upstairs na farko a gidan Papi shi ne sashinsa da matarsa Mom Hajiya Sa'adatu, ɗaya upstairs ɗin kuma shi ne na Affa General da Momsee Hajiya Huraira, sai haɗaɗdun flat ɗin kuma ɗaya na CAS Bunayd, ɗaya na Suhail da Nabeel. Duk da Bunayd yana da part nasa a gidan, amma sai bai ko je ba ya tsaya a sashin Affa General, anan da masu aiki suka kawo abinci, Momsee ta saka su Ramla suka yi saving nasu, cikin nistuwa suka ci, sannan kowa ya shige ciki dan ya wasta ruwa, Bunayd na miƙewa Majeeder ta miƙe ta rufa masa baya, juyowa yayi ya kalleta ya ɗaga mata gira ɗaya ya ce, "Autan dole ya aka yi?" Tura baki Majeeder tayi ta ce, "Ni dai ƙafanka ƙafa na, sai ka ƙara guduwa irin na lokacin kuma ka jima ba ka zo ba." Murmushi Bunayd yayi dan ya tuna wayon da ya yiwa Majeeder ya samu ya koma Lagos, last time da ya zo, bai ce komai ba ya riƙo hannunta ya ce, "To Autan dole muje sai ki bani labari ma, amma dai wanka zan yi, kuma nan gaba matata ta ga kina maƙale mini haka haushinki za ta dinga ji, ba ruwanta da ke ƙanwata ce." Majeeder maimakon ta ɓata rai sai ta yi dariya ta ce, "Yauwá sweet bro yaushe za ka yi aure? Ai na faɗawa Papi ya faɗa maka zan zauna a gidanka idan ka yi aure, sai shi kuma ya ce na faɗa maka ka yi aure." Bunayd darawa yayi ɗan dai-dai sannan ya ce, "Autan dole ba wayo, kar ki damu zan yi aure soon, yanzu dai ki taya ni nemo matan kin ga ban da budurwa." Majeeder har da stallenta an ce ta taya sa nemo mata, "Sweet bro ka yi wanka ka zo na shafa maka wani labari." Bunayd dariya yayi ya shige ɗakinsa da ke sashin Affa General, Majeeder kuwa ta zauna tana jiransa, tana ta danne danne a wayansa, photo's take ta kallo, wani idan ta gani sai dai ta dara, har Bunayd ya gama wanka ya shirya, sannan ya mata magana ta shiga ɗakin ita ma, zama tayi a kan gadonsa ta ce, "Sweet bro ban ga photon kowa a wayanka ba balle na taya ka zaɓan matan." CAS ya ce, "Autan dole ai ke za ki nemo mini, amma fa bana son masu saka hijabin nan, wacce dai ta waye hakan nan, ta fi ki wayewa fa, dan ke nistasttiya ce." Majeeder dariya tayi ta ce, "sweet bro wasa kake mini ko." CAS Bunayd ya ce, "To bani labarin da kika ce za ki bani, tunda ba za'a barni na huta ba za'a cika ni da hira." Murmushi Majeeder tayi ta ce, "Da ɗumi-ɗuminta ai ta fi yaya, kar ta huce makwabta su ji baka ji ba, kuma kai ne baka zuwa shiyasa ba zan iya haƙura ba." "To nidai bani labarin dan bacci nake so nayi" CAS ya faɗa yana kwanciya a gadonsa." Majeeder ta ce, "albirshir yaya." "Goro fari tass kaman Suhaila ba kaman ke ba." Cunna baki Majeeder tayi, sai an ce bata da haske sosai ita, cewa tayi, "To Papi ne ya ce mini zai kawo mini Aunty kuma Mami zan dinga ce mata, kuma har da ƙawa za ta taho mini da ita, yanzu ai ba dan ƙawata ƙanwarka ba ce, da sai ka aureta, ni nasan mai kyau ce ita daga sunanta, Faɗima Banafshaaa, kuma fa ita ma wai a musabaƙansu ita ta zo ta ɗaya." Bunayd ɓata fiska yayi ya ce, "tashi ki tafi zan yi bacci." Majeeder sturut! Ta miƙe ta ce, "Na tafi da wayan sweet bro sai ka tashi." CAS idanuwansa a lumshe ya ce, "je ki da shi." Majeeder juyawa tayi ta fita da wayan, ita bata lura da yanayin Bunayd ma ya sauya ba akan magananta, shi kuma guntun tsaki ya ja ya ce, "To ban taɓa tsanan mutum ba, amma har kin saka naji haushin yarinya na staneta, ni ma haɗina da Ustaziya wacce har musabaƙa take yi" yana cikin magana sai ga kira ga shigo a ɗaya wayansa, yana mita ya ɗauka bai ma duba waye ba ne. Maganan da aka yi a ɗaya ɓangaren ne ya sa shi dan taɓe baki, cikin yaren Yoruba yayi magana, ya ce, "aikinka ya jima da kammaluwa, mun yi magana da baturen, sun amshi contract ɗin." Mr Sonny Yoruba, a ɗaya ɓangaren cewa yayi cikin Yorubanci, "Ok nagode CAS, yaushe za ka shigo? Ko kuma ni yaushe kake free na shigo." Taɓe baki CAS yayi ya ce, "ina Kano kuma zan yi kwanaki, duk abinda ake ciki ka ƙira ni ko kuma ka mini magana ta WhatsApp kawai...", Haka suka gama tattaunawa suka yi sallama. Bunayd ya gyara zai yi bacci sai ga ƙiran Abeed, guntun tsaki ya ja ya ɗauka tare da karawa a kunne ya ce, "Jarababben Ango ya aka yi? Ka bi ka dameni da kira ina hutawa, idan kai maye ne fa ka kama kurwan mutum to sai ka kashe mutum zai samu sukuni." Abeeb taɓe baki yayi a nasa ɓangaren ya ce, "Da alaman dai wani ya taɓo ka, ba sallama sai surutu haka, duk da daman kai kanari ne, to faɗa mini me ya faru." CAS ajiyan zuciya ya yi sannan ya ce, "Yanzu Majeeder ke shirin ɓata mini rai wai ai Papi zai ƙara aure kuma za a taho mata da ƙawa." Dariya Abeed yayi ya ce, "Soyayyan Mom ta mosta kenan, shi ne kake taya ta kishi, dan za'a mata kishiya." Bunayd taɓe baki yayi ya ce, "Ina ruwana da Mom balle dan za'a mata kishiya ya dame ni, ni ai so nake mu yi maganan da Papi naji idan gaskiya ne to ni na ɗau nauyin kayan aure da sadaki da komai ni zan masa, Allah sa ya samu wacce ta fi Mom hali mai kyau." "To me damuwanka da ka ce Majeeder ce ta ɓata maka rai" faɗin Abeed yana murmushi. CAS ya ce, "Wai ƙawar da za'a zo mata da ita ne take cewa da sai na auri yarinyar dan ita ma har musabaƙa suke kuma ta ɗaya ta zo, ni ina ruwana da Ustaziya, ai Ustaziya sai ustaz, mu dai da muke ƴan jagaliya sai mata ƴan irin mu." Dariya ishashshe Abeed yayi ya ce, "To me abin damuwa a nan? Ai naga kai ma ɗin haddan ƙur'ani ne a kanka, Kuma abin addini babu wanda ba ka ƙoƙari a kai, to kuma duk da hakan ga ka ɗan jagaliya, ja'iri ɗan gidan General ba, to dan tana da ilimin addini mai zai sa ta zama ba yanda kake so ba, ni har naji haka kawai ta shiga rai na, ba dan ina da tawa ba, ai da na yi wuff ta ita." Staki Bunayd ya ja, ya ce, "Sai kuma ka yi ai, ni dama ji nayi na staneta ma, dan haka sai ka yi ta biyu da ita." Dariya Abeed ya saka, Bunayd ya taɓe baki ya ce, "sunan wani wai sallau, wa ya ga saliha da ta zarce, ni wayayyiya nake so wacce dai ba jahila ba, amma dai addini bata mata overdose ba, dan haka idan ta so ma zan juye mata na kai na, kawai ta zama ba nistasttiya ba, kuma ba ta gari ba, ba saliha ba, kuma ba kamila ba, indai ita musulma ce mumina shikkenan, kai ni fa tun da Allah bai haramta auran ahlul kitab ba, to zan iya auren alhul kitab indai ta waye yanda ya kamata, kuma ta san rayuwa." Dariya Abeed yayi ya ce, "Gaskiya Musulmin ɗan jagaliya ɗan gidan General, kana abinda kake so, to wa ya ce maka yanzu akwai nagari? Ai kowa tafiya haka kawai yake kaman ɗan iska a gantale, ai duniyan yanzu ba'a niste take ba balle a samu wani na gari, kowa ɗan iskan kansa ne kawai shiru ake, yanda rayuwa ta zama ai kowa ba dan storon Allah ba sai ya koma bariki iskanci ba mai yin aure, ko kuwa a fara fashi da rana tsaka, kai dai addu'a za ka yi dan ba'a hijabi kamila take ba, sai ka dage baka son salihar mace kuma sai ka ga wacce ka samu ɗin duk da a zahiri ba saliha ba ce, amma ba lallai ta maka abinda kake so ɗin ba, kuma sai ka ga salihar ta maka dunuyancin da kake so." Bunayd murmushi yayi ya ce, "Na dai gane me kake nufi, wato dai so kake ka ce kamilarka tasan rayuwa, to ba dai zan sauya maganana ba, atou tantiriya nake so." Abeeb murmushi yayi ya ce, "Ko ma menene kai ka jiyo, ni dai na ce Allah baka mace tagari saliha mar'atussaliha" ya ƙarishe yana dariya. Bunayd ya ce, "Ba Ameen ba dan uban mutum." "To yaushe za mu haɗu ne? Kada na zo ka ce kana hutawa na san ka da renin hankali" faɗin Abeed. Bunayd ya ce, "Yau ba inda zan je kuma ba wanda zan saurara hutawa zan yi muna hiranmu da Majeeder, Papinmu zai ƙara aure, za'a yi wa Mom tamu kishiya ka ga sai mu fara shiri." Dariya Abeed yayi ya ce, "ka ji ɗan banza yaro mara taya mamansa kishi ba.." Hiransu suka yi suna ta kwalala dariya, har suka yi sallama Bunayd ya kwanta baccinsa. Kowa hutawa yayi ba wanda ya je ko ina, su Suhail da Nabeel suna sashinsu, Bunayd kuwa yana maƙale a sashin Affa General hankalinsa kwance, ko sashin Papi bai je ba, shi kuwa Papi ya bari su huta tukunna, bai je sashin Affa ba kuma bai nemi su zo ba, ita kuwa Hajiya Sa'adatu tana cike fam kaman za ta fashe, mutum da yaronsa an mallake masa shi, yaro yana Lagos yana wajansu, ya zo ma yana sashinsu, ko zuwa ya gaisheta bai yi ba balle ya nemi albarkan ta, sai mita kawai take yi, kuma ga Majeeder ma ta je wajansu ta maƙale, Papi kuwa ko ta kanta bai bi ba yana yin abinda ya damesa ne kawai, dan shi akan haka ba ya ganin laifin Bunayd, ko me yayi ita ta nema tunda tun farko ita ma bata sauƙe nata haƙƙin na mahaifiya ba. Sai washe-gari bayan sun karya kowa ya yi wankansa ya ci kwalliya kaman masu zuwa dinner, sannan dukkansu suna nufi sashin Papi, CAS da farko ya ce ba inda zai je, sai da Affa General ya nuna za su ɓata sannan ya yarda zai je, amma dan Papi zai je ba dan Mom ba. Bayan sun shiga kowa ya samu waje ya zauna, Papi sai murna yake ganin dukkansu da iyalansa ga su, sai yake ji a ransa ina ma har da Ramlatunsa da sai ya fi haka farinciki. Mom sai wani shan ƙamshi take, tana kallon banza wa Momsee, ita dai Momsee ko a jikinta dan bata san ma tana yi ba. Taro CAS Bunayd ya buɗe musu da addu'a, duk suka gaggaisa, shi ma ya gaishe da Mom, ta amsa a daƙile tana cewa, "tunda an mallakeka ai dole ka dinga gaishe ni kaman ba ni ce na stugunna nayi naƙudanka ba." CAS bai ce komai ba, kuma hakan ya yiwa Papi da Affa daɗi, Papi ne ya kalli Mom ya ce, "Sa'adatu ki iya bakinki." Mom kawar da kai tayi kawai. Papi faɗa ya yiwa yaran sosai, ya musu nasiha, Affa General ya faɗa wa Papi abinda Suhail yayi na ƙin aikin soja, sannan ga Nabeel ma yana son bostarewa. Murmushi Papi yayi ya ce, "Wannan ai stakaninsu da mara jin yayansu ne General ba sai ka sako ni ciki ba." General ya ce, "ai my Man ya musu magana sun ƙi ji." Bunayd shafa kai yayi yana kallon Papi yana danne dariyansa, su Nabeel kuma dariya suka yi dan sun san indai dan Affa General ya kare yayansu ne, to ba abinda ba zai ce ba. Papi ya ce, "To Shikkenan tun da sun ƙi jin nasa maganan, sai a ƙyale su kawai su yi kasuwancin, shi Bunayd ɗin ai yayi soja ya gajeka sai ka godewa Allah, nima a bar mini yarana su yi kasuwanci irin nawa su gaje ni." General murmushi yayi ya ce, "Shikkenan ai tunda ka ce haka yaya, Allah taimaka ya basu sa'a." Duk suka amsa da Ameen, Nabeel farinciki kaman yayi stalle, ya ce, "Papi Allah bar mana kai." Affa General ya ce, "Ni kuma Allah ya kashe ni ku huta ko?" Bunayd miƙewa yayi ya ce, "Ai General kai ne ma mai lasting ɗin, Allah bar mana ku ya ƙara girma ya saka muku da aljanna, Allah bar mana General da Momsee kawai, Papi kuma ni zan masa gudumawa" yana gama faɗa ya fice. Papi dariya yayi, dan yasan ba zai wuce Majeeder ce ta shafawa yayan nata ba, su General dai dariya suka yi ba su gane nufin CAS ba, Mom kuwa ƙwafa tayi kawai, duk da bata shaƙu da Bunayd ba, amma yanzu ƙaunar yaronta take yi, bata jin za ta iya faɗan wani mugun abu a kansa balle ya shiga wani hali tunda ta haife sa komin yaya bakinta zai iya kamasa, sai dai idan mugun fata yake mata ba kishiya to zata nuna masa ita ce mahaifiyarsa tana da iko da shi kuma. Wuni suka yi cikin nishaɗi, Papi da Affa sai ƙara tattaunawa suka yi akan abinda ya kamata. Sai da su General suka yi sati guda, sannan suka tattara suka koma Lagos, Bunayd ma ya bi su dan sun gama maganan komai na bikin da Abeed, yanda komai zai tafi, dan a ranan da suka koma Lagos a ranan Abeed ma ya wuce Adamawa. Papi sai sati na sama zai yi tafiya nasa, amma kuma busy ya ƙi barinsa ya je ya kalli masoyiyarsa kamun ya tafi tunda har wata biyu zai yi, sai waya kawai suka yi ya tura mata duk abinda ya kamata, kaman yanda ya faɗa dai bai ƙara mata maganan aure ba, sai dai ya mata faɗan ta kula. Majeeder ta bi su Affa General sun koma tare, Hajiya Sa'adatu kaman za ta haɗiye rai dan masifa, Alhaji kuwa ya ce tunda yarinyar sa ce shi ya ga daman ta bi su, idan abun bai mata ba ta yi zuciya ta haiho wata yarinyar ko wani yaron, Hajiya cikin masifa ta ce ita ta gama haihuwa da shi idan ya ga dama ya sayar da yaran. Papi ko sati guda bai yi ba saboda ɓaci ran da Hajiya ke cusa masa, haka ya tattara ya tafi tafiyansa abunsa, Suhail ma bai kai sati ba ya koma Turkish ɗin sa, Nabeel kuwa Bunayd ya masa komai da ya kamata a Spain ya ci-gaba da karatunsa a can, shi ma yana zaune a gidan Bunayd. Rayuwa na tafiya ta ko wani ɓangare lafiya sai godiya ga Allah inda yanzu haka auren Abeed saura sati guda, kuma CAS Bunayd ya shirya tare da su Suhaila, Ramla, Majeeder da Nabeela duka ya taho da su, sun ce su ma za su zo da bikin. Suna isowa yayi magana da Abeed ya kai su Majeeder gidan su Nusaiba Amarya, ta tarbe su hannu bibbiyu, duk anko da ake da komai Bunayd ya yi musu, ana fara shagalin biki kuwa kullum da kansa yake kai su wajan event ɗin da za'a yi kuma ya basu kuɗi a hannunsa, duk abinda ya ke yana zuwa da sauran abokanansu da suke gari, idan ka ga shungullan da Bunayd ke yi za ka ɗauka shi ne Angon, sosai Bunayd yake da kirki kuma ba shi da girman kai. Yau take Thursday wanda a washe-gari juma'a za'a ɗaura aure, kuma sai washe-gari Ango zai zo, yana can Adamawa a wani daji gaba da Michika kamun a isa Mubi, shi da abokanan aikinsa suna fama da ƴan ta'adda masu addabar mutane sai dai mu ce Allah ya ɗaura su a kan su. Ɓangaren Amare yau walima ake yi, Bunayd ya kai su Majeeder da suka sha Arabian gown's suka shuka yi kyau Masha Allah, yana sauƙe su ya miƙa musu kuɗi ya ce, "Ku ji wa'azi mai kyau kuma ku yi aiki da shi." Suhaila ce ta yi dariya ta ce, "yaya dama ai indai ka ji wa'azi dole ka yi aiki da shi, musamman idan ka zo dan wa'azin ne." Bunayd girgiza kai yayi ya ce, "wa ya faɗa Miki? Ai da yawa mutane suna jin wa'azi ne kawai ba aiki suke da shi ba, a cikin malamai wasu masu yin ma ba wai suna yin abinda suke faɗan ba ne, shiyasa aka ce ka yi abinda Malam ya ce ba abinda ya yi ba, dan haka ku ɗauka kuma ku yi aiki da shi." Nabeela murmushi tayi ta ce, "Inshà Allah yaya za mu ɗauka mu yi aiki da shi." "Good! Nabeela my love" Bunayd ya faɗa yana murmushi. Majeeder ta ce, "yaya ka zo da wuri ka kai mu yawo." Bunayd ya ce, "ku mastalanku kenan ba'a haɗa hanya da ku, yara sai son yawa, to driver ne ma zai zo ya ɗauke ku ba ni ba" yana faɗa ya yiwa motansa key ya tafi. Duk tura baki suka yi suka shige, sannan suka samu waje suka zauna, wa'azi ne ake mai kyau mai kuma rasta jiki, wanda ba iya Amarya zai amfana ba, duk wata mace da ta ji ta yi aiki da shi to zai amfane ta duniya da lahira, dan misali ake mana da rayuwan da Nana Faɗima AS ta yi a gidan mijinta sayyadina Ali AS, dan haka mata wannan kyakkyawan tunatarwa ce gare mu, ki duba Allahn da ya ce a zauna a gidan miji a yi haƙuri, ki kuma aro halayyan Nana faɗima AS za ki ji daɗin zaman gidan miji, kuma za ki yi alfahari da hakan duniya da lahira, Allah ya sa mu dace, ya ƙara mana zaman lafiya a dakunanmu, ƙannenmu da yayunmu, da yaranmu, da iyayenmu marassa aure duk Allah ya haɗa su da na gari ya kuma ba su haƙurin zama. Duk kwanakin nan da Bunayd yayi a gidansa na Kano yake kwana, iyakacinsa da gidan Papi idan ya zo ɗaukan ƙannensa ko ya dawo da su, Hajiya Sa'adatu ita haka ya mata ko babu komai tunda dai ya baro su General, bata san biki ne ma ya kawo sa ba, shi kuwa idan ya zo zai gaisheta zai mata ladabin da ya kamata, kawai dai baya sakewa da ita ne, dan Bunayd na da ilimi kuma yana aiki da iliminsa, ya san ita mahaifiya ce kuma yasan haƙƙinta da ke kansa, sannan ya san hannunka ba zai ruɓe ka yankesa ka yasar ba, uwa ta wuce wasa. Bayan Bunayd ya baro wajan su Majeeder, yana cikin driving ƙira ya shigo wayansa, ganin layin Abeed sai ya ɗauka yana murmushi ya ce, "Palace is loading, Ango mai jiran gado, Dragon za'a sha aiki" ya ƙarishe yana dariya. A maimakon ya ji muryan Abeed sai ya ji muryan wani daban, hankali a tashe yake magana ya ce, "Bunayd an samu mastala fa." Bunayd ya ce, "Me ya faru? Ina shi Captain Abeed ɗin?" Wanda ke maganan ya ce, "Wallahi a tarzomansu da ƴan ta'adda shi ne aka samu akasi, duk da mun gama da su amma dai an harbesa, mummunan rauni ya samu kuma daman ya ce, duk abinda ya faru kai kaɗai za'a kira kar a faɗawa iyayensa." Hankali a tashe Bunayd ya ja wani wawan birki ya ce, "Yanzu kuna ina?" "Muna babban asibitin cikin Mubi." Bunayd bai jira ƙara jin komai ba ya kashe wayansa ya juya sai airport, hankali tashe yayi duk abinda ya kamata, jirginsu ya ɗaga sai Adamawa, jirginsu na sauƙa daman ya riga ya gama magana da sauran abokanansa da ke nan a air force base na cikin jimeta, mota aka turo mata da drivern da zai kai sa har cikin Mubi, ba ɓata lokaci suka kama hanya, suna tafiya amma Bunayd gani yake basa isa da wuri, tun da yake bai taɓa wuce cikin Adamawa ba, ba local government da ya sani, bai san nisan Mubi ya kai haka ba, ji yake kaman ya fire ya gansa a gaban abokinsa. ⭐ Yau Lahadi Banafsha ta warke daga cutan period ta yi rass abinta ta gama, wanka ta sha sharr da ita suna zaune da Mami suna hira kaman ba komai, sallama suka jiyo, wanda daga ji Banafsha ta gane muryan waye ne, zuciyanta ne ya stinke sai kuma ta saki murmushi lokaci guda, Mami dubanta tayi ta ce, "amsa sallaman mana, ki je ki duba waye ne." Miƙewa nayi na shige ɗakina na sako hijabi sannan na fito na wuce, kaman yanda na zatan kuwa shi ne, Malam Abbo ne, murmushi nayi tare da yin ƙasa da kai na tare da masa sannu da zuwa, amsawa yayi, na ce masa ina zuwa, sai na koma cikin gida na faɗawa Mamina Malam Abbo ne, murmushi tayi ta girgiza kai kawai ta ce, "Sai ki ce ya shigo ko." Komawa nayi na masa iso, muka shigo palourn lokacin Mamina ta riga da ta shige ɗakinta. Malam Abbo zama yayi ni kuma na wuce na kawo masa ruwa da abinci duka, yau ma kaman ranan murmushi yayi ya ce, "Lallai ni ɗan gata ne kullum har da abinci, ki ce idan zan zo zance za daina cika cikina da tuwon Ummina." Murmushi nayi tare da yin ƙasa da kai na ban ce komai ba. Ƙara gaisawa muka yi bayan ya sha ruwa, sannan na ce, "Malam a yi haƙuri wannan satin ban samu zuwa ba, na faɗawa Umaima ta faɗa banji daɗi ba ne." Murmushi Malam Abbo yayi ya ce, "To ai ni yanzu ba abinda ya shafi makaranta bane ya kawo ni, batu ne akan rayuwata, farincikinka, cikar burina, muradina, maganar soyayyata da ƙauna ce ta kawo ni Sayyadata Roohi ta." Wani kunya ne ya rufe Banafsha da ya sanyata kulle fiskanta da tafin hannunta, wani irin soyayyan Malam Abbo ne ya stirga mata duk wani sassa na jikinta lokaci guda ba zato ba tsammani, sai dai kaman daga sama take jin maganganun Maminta na dawo mata, sai kuma wani damuwa ya maye gurbin farincikin, wanda har Malam Abbo sai da yayi mamakin ganin yanayinta ya sauya sosai, ba tare da ya ankara ba ya kuma jin tana cewa, "Malam Abbo ka yi haƙuri, abinda na faɗa maka da farko shi ne har yanzu, ba zan iya aure da mugun tabon da ke tare da ni ba" ta na ƙarishe maganan kaman zan yi kuka, saboda ni da kai na ina jin ciwon abinda nake faɗa. Malam Abbo murmushi yayi ya ce, "Ni ma kuma ina kan baka na, ina ƙaunarki har gobe, duk wannan amsa naki ban gamsu da su ba Roohi, amma zan yi abinda ya kamata, sai dai dan Allah ko ne na yi kada ki ga laifina soyayyanki ne ya ja." Shiru nayi ban ce komai ba, saboda kokawa nake da zuciyata na samu da rashi da nake gani a filin Allah. Malam Abbo ba tare da damuwan komai ba ya ce, "kwana biyu Umaima ma bata ke makarantan ba, fatan dai lafiya?" Cikin damuwa na ɗago kai na, amma muna haɗa ido sai naji wani iri, tuni nayi ƙasa da kai na na ce, "Amma bansan me ya sameta ba, bansan ko wani abun ya faru ba, dan nima yau ne naji daɗin jikin nawa, sai dai in Allah ya yarda gobe da safe zan shiga na dubata kamun mu wuce makaranta." Jinjina kai Malam Abbo yayi ya ce, "Hakan ma yayi Sayyadata, Allah ya yarda ya kuma nuna mana da rai da lafiya, sannan kuma Allah nuna mana bikinmu, ranar da Malama Faɗima za ta zama mallakin Aliyu bawan Allah." Shiru na yi ban kuma cewa komai ba, Malam Abbo dai sai hiransa yake mini na soyayya, duk da ina jin daɗi da kuma sanyi a rai na amma na kasa nuna hakan dan bana son na yaudari malam Abbo ko kaɗan, sai da lokaci ya ja idan yayi magana sai dai na ce Uhmn! Ko uhun!, Ganin dare na ƙoƙarin yi suka ya dube ni yana sakar mini murmushi wanda yake daga zuciyansa ya ce, "Nikam zan tafi Sayyadata sai na ƙara zuwa kuma." Ba tare da na kallesa ba na miƙe na ce, "Bari na ƙira Mamina ko gaisawa ba ku yi ba." Murmushi Malam Abbo yayi ya ce, "Umma ta zama surkuwata kunyarta nake ji, ki bari zan zo daga baya na gaisheta daban, yanzu kunya nake ji dan yau wajanki na zo." Abinda Malam Abbo ya faɗa dariya ya bani, dan haka murmusawa nayi, kawai muka yi sallama na rakasa har ƙofan gida, kallona yayi ya ce, "Ina matukar ƙaunarki Sayyadata." Kallon juna muka yi na ƴan second's, inajin kaman na faɗa abinda ke rai na, amma ba dama, ganin kuka na neman zuwa mini sai na juya da sauri na kulle ƙofa na koma ciki. Malam Abbo murmushi yayi dan shi ya riga ya sanya a ransa indai Faɗima rabonsa ce to zai sameta, yasan mai zai yi, in Allah ya yarda zai mallaketa. Ni kuma ina share hawayena na shige ciki, kusan karo muka yi da Mamina, girgiza kai tayi. Mamina ta ce, "lafiya kuwa? Me ya faru? Me ya sameki? Yanzu nake cewa bari na bi bayanki kin zauna a waje me ya faru?" Share hawayena nayi na seta kai na, cikin dakewa na ce, "Ba komai Mami." Ganin dare yayi duk yin Mami, sai ta ƙyale kawai ta wuce ɗakinta na wuce nawa, ina addu'an Allah ya sa lafiya an ce Umaima ita ma kwana biyu ba ta je makaranta ba, da tunanin haka na kwana a rai na. Masu Sharhi ina matuƙar Godiya 👏 Uwar batoorl taku. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKI NE Surayyatou nah اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 BUNAYD: is a name use for baby boy's, that mean's sᴛʀᴏɴɢ, sᴛᴏʀᴍʏ ᴀɴᴅ ᴘᴏᴡᴇʀғᴜʟ, and also is a name that identify a specific ethnic, like halimatu-sa'adiya, the real name is halima, sa'adiya is her ethnic name. Bunayd or Bunaid, in other face mean is ethnic name which located in Pakistan, in Muslim's society, the name is usually use as nick name for those with name Muhammad. The name origin is Pakistan. 🅿️ 66 _ 70 Washe-gari da safe na shirya tafiya College da wuri, bayan na gaishe da Mamina ta amsa, sai na ce, "Mami zan bi gidan su Umaima kamun na wuce, Malam Abbo ya ce mini ita ma kwana biyu ba ta je makaranta ba, bansan ko me ya sameta ba." Mami ta ce, "To a dawo lafiya, ki gaishe su, sannan ki kula sosai ko." Ɗaga kai na nayi alaman na ji, sannan na mata sai na dawo na fice, ina ƙoƙarin shiga gidan su Umaima sai ga ta ita ma ta fito da shirin zuwa College, murmushi muka sakarwa juna, na ce, "Umaimatyna." Murmushi Umaima ta mini wanda hankalina bai kwanta da shi ba, ina tunanin ma na ƙarfin hali ne, bata ce mini komai ba kawai ta riƙe hannuna muka yi gaba, ni bin ta nake kaman mara lafiya dan jikina yayi sanyi, bansan me yasa tayi haka ba, amma dai na yi shiru, muka nemi mashine muka tafi College. Mun wuni a makaranta muna ta lecture's, amma kwata-kwata na kasa ganewa Umaima, gaba ɗaya bata son yin magana sosai, ƴar rigiman da muke yi da stokanan juna duk yau babu, sai dai murmushi kawai take mini idan na yi magana, kasa jurewa nayi da hakan, ana tashinmu muna tafiya kan mu samu mashine na ce, "Umaima me ya faru? Me na miki? Ko ba ki da lafiya ne?" Mashine ta tare mana muka shiga, ƙara kallonta nayi na ce, "masoyiya me ke faruwa dan Allah?" Umaima murmushi ta sakar mini ta ce, "Me ne kika damu kanki haka Banafshaty, lafiya fa ba komai." Kallon Umaima kawai nake yi ba dan na yarda da abin da ta faɗa ba, numfasawa nayi na ce, "To me ya hanaki zuwa makarantan tahfiz kwana biyu?" Nan ma shiru Umaima tayi bata ce komai ba har muka isa gida, mashine na ajiye mu ta kalleni da murmushin ƙarfin halin da take mini tun safe ta ce, "Banafshaty ki gaisar mini da Mami", ta faɗa tare da yin gaba ta shige gidansu. Haka Umaima ta tafi ta barni a staye a gantale ta shige gidansu, sai da na gaji da tsayuwa sannan na numfasa na juya cikin damuwa na shige namu gidan. Mamina na samu zaune a palourn tana waya, jakana na ajiye a kan kujera na shige jikin Mamina na lafe, ba tare da na ankare na bacci ya fara yin gaba da ni, sai da Mamina ta gama wayan da take yi sannan ta shafa kai na ta ce, "Fatu kulen Maminta, shugabar masu son jiki tashi kada ki karya ni." Ni kuwa tuni na fara bacci ban ma ji me Mamina ke faɗa ba. Mami sunkuyawa tayi ta kalli fiskana, ganin bacci na fara sai ta murmusa ta girgiza kai kawai, a hankali ta bubbuga bayana ta ce, "tashi kije ki cire kayan makarantan, idan kin wasta ruwa sai ki kwanta ki yi baccin, dan da alama yau kin ajiye wanda zai je miki tahfiz ɗin." Cunna baki nayi, cikin shwagaɓa na ce, "Mami jikinki ne daɗin kwanciya shiyasa na ji bacci." Murmushi Mami tayi ta ɗaga ni, amma na koma na lafe na ce, "Mami yau bansan me ya samu Umaima ba, magana ma da ƙyar take mini." "Ba sai ki tambayeta ko wani abun ya faru ba Banafsha" faɗin Mami tana ɗaga ni. Zama nayi sannan na ce, "Mami wallahi na tambayeta, da farko ta yi shiru, daga baya ta ce ba komai." "To wataƙila ko bata jin daɗine, ko kuma wani abun daban, amma ki bata kwans biyi idan ma bata da lafiyane Inshà Allah za ta ji sauƙi, kuma za ta faɗa miki, kada ki damu kanki kinji ƙawar Umaima." "Uhmñ!" Kawai na faɗa na miƙe na ɗau jakana na shige ɗakina, sai da na cire uniform na watsa ruwa, sannan na fito na ɗau abinci na cika cikina, sai na koma na kwanta, kamun lokacin tahfiz yayi. Yamma na yi na tashi na shirya, nan ma a ƙofan gida muka haɗu da Umaima, yanzu ma yanayinta kaman ɗazu da safe, haka har muka isa tahfiz, mun yi karatu har aka tashemu, sannan muka kamo hanyan gida, muna tafiya sai ga Malam Abbo, ba daman na ɓata rai ko wani abu, murmushi ya sakar mini ya ce, "Sayyadata ina zuwa anjuma." Tura baki nayi na ce, "ka yi haƙuri Malam zan yi aiki." Ba tare da damuwan komai ba Malam Abbo ya amsa da shikkenan ba mastala, ya juya abinsa, mu ma muka yi gaba, Umaima murmushi tayi ta ce, "Sayyadar Malam Haidar." Taɓe baki nayi na harare ta na ce, "Tun da kin ƙi faɗa mini abinda ke faruwa, ba ruwana da ke kada ki mini wani magana " Murmushi ta kuma yi ta ce, "To Allah ya sanya alkairi Banafshaty, Allah kuma ya tabbatar da alkairi, ashe da tabbata gaskiya ne hasashen ɗalibai." Ban ce mata komai ba, muka cigaba da tafiya har muka isa gida, Umaima ta shige gidansu, nima na shige gidanmu. Haka muka kwashe kwanaki har muka cinye wannan satin yanayin Umaima ya ƙi sauyawa, kuma ta ƙi faɗa mini abinda ke faruwa, sannan a gefe guda kuma Malam Abbo kullum sai ya takura akan zai zo, ni kuma sai na dinga kawo masa uzurina duk saboda bana son ya zo, ni bana buƙatar shaƙuwa sosai ya shiga tsakaninmu, dan kada ma gaba idan na nuna bansan zancen ba, shi kuma ya ce na yaudaresa. Yau da yake Friday ne muna da class na ƙarfe bakwai, da wuri na shirya, muka haɗu da Umaima a ƙofa yanda muka saba haɗuwa kwanannan, mashine muka shiga ya kai mu makaranta, mun yi lecture's har lokacin sallahn juma'a yayi aka fita kamun a sauƙo juma'a kuma. Ni da Umaima daman ba damuwa muka yi da zuwa masallacin school ba, dan haka alwalanmu muka yi, muka yi sallahnmu a ƙasan wani bishiya mai inuwa inda muke zama, sai da muka idar sannan na kalli Umaima cikin damuwa na ce, "masoyiya dan girman Allah dan darajan Annabi ki faɗa mini abinda ke faruwa, idan ma wani laifi na miki ai sai na baki haƙuri, idan wani abun ne ai gwanda na sani zai fi, masoyiya ki tuna fa, duk abinda ke faruwa da ni kin sani, wanda ba ki sani ba ma ina sanar da ke, mastayin Aminiyata na baki, banda wacce zan nuna na ce ƙawata ce sai ke, masoyiya da ke nake shawara, ke ce abokiyar kukana kuma abokiyar dariyana, to me ya sa abu zai faru ke ba za ki faɗa mini ba, sai ki dinga shashshareni, ko dai ke ba ki bani mastayin da na baki ba ne?" Na ƙarishe maganan ina kallon cikin idanuwanta. Umaima murmushin da ya fi kuka ciwo ta yi, bata ce mini komai ba sai hijabinta da ta ɗaga ta nuna mini dansten hannunta, ban dawo daga duniyan da nake ba ta kuma nuna mini gadon bayanta, cikin damuwa na ce, "Umaimaaaa!! Me ya same ki? Wannan shatin bulala ne fa, wa ya miki wannan duka? Naga dai banji mostin Ya Danish ba wannan weekend ɗin, dan Allah me ya sameki Umaima" na faɗa kaman zan yi kuka. Murmushin Umaima ta kuma yi, ta buɗe baki za ta yi magana kuma sai ga hawaye, ganin kukanta nima sai hankalina ya tashi, ga shi dai-dai lokacin malamai sun sauƙo juma'a, an koma mana aji, haka na lallasheta muka koma class. Sai wajan ƙarfe biyar aka tashemu, muna fitowa class Umaima ta labarta mini abinda ya faru har kwanciya a asibiti da ta yi, tana bani labarin har muka samu mashine muka shiga, ni kuwa cikin tausayi da damuwa nake sauraranta, uwa dai uwa ce amma wani abun sai a hankali, lallai dole Allah ya ce a duk halin da kake ka gode masa, kuma kowa da tasa jarabawan da Allah ke jarabtansa, ga ni dai mahaifiyata tana rayuwan da ba kyau har ana ƙirana ƴar karuwa, ina damun kai na bayan wannan shi ne jarabawana, indai Mami ta sa hannunta a jikina to fa ni ce na nema, garin faɗa mata gaskiya na faɗa mata maganan da bai mata ba, amma bayan haka Mami ko hararana bata yi, to ga Umaima wacce mahaifiyarta ba ta da wani mugun tabo, tana da mutuncinta a gidan aurenta, amma akan abinda bai kai ko stawa a yiwa mutum ba, Umma ta mata wannan mugun duka, to Allah kyauta ya raba mu da iyayenmu lafiya. Mashine na sauƙe mu, muka fara tozali da Ya Danish zaune a bayan motansa idanuwansa a kan hanya kaman mai jiran isowan wani abu, ina ganinsa na ji gabana ya faɗi haushi ya turnuƙe ni, tuni na haɗa fiska ko kallonsa ban yi ba muka yi sallama da Umaima na shige gidanmu, ita ma ta shige nasu gidan bayan ta gaishe da Ya Danish da idanuwansa ke kai na. Malam Abbo da ya gaji da bin Banafsha zai zo zance, ta ƙi basa dama sai abin ya damesa, dan haka daman yana da shirin yi wa Mami magana akan Banafsha, sai ya shirya staff abinsa, yana dawowa sallahn juma'a ya nufi gidan Mami, cikin takunsa na nistuwa yake tafiya har ya isa, da kansa ya shiga gidan yayi sallama. Mami da ke zaune a palour ta sha wankan juma'an ta, amsa sallaman ta yi ta yafo mayafinta ta leƙo, ganin Malam Abbo ne tana murmushi ta ce, "Kai ne Malam Haidar." Malam Abbo da fara'a yana sunkuyar da kai ya ce, "Nine Umma, barka da gida." Mami ta ce, "ka iso ko." Malam Abbo bayan Mami ya bi ya shiga palourn, stugunnawa yayi zai gaisheta sai Mami ta ce ya zauna bari ta kawo masa ruwa, yana cewa da ta bari, amma Mami ko nuna ta ji bata yi ba ta wuce, ta kawo masa abun sha, sannan ta zauna, Malam Abbo durƙusawa yayi ya gaisheta. Mami ta amsa tana murmushi ta ce, "Sannunka da zuwa Malam Haidar, ya kuma haƙuri da su Faɗima." Malam Abbo baki kaman zai yage dan murmushi, sai sunkuyar da kai yake yi irin ana gaban surkuwan nan, cewa yayi, "Ba komai Umma, Allah ne da haƙuri da mu, Malama Faɗima yanzu kam Masha Allah, kwana biyu da bata zo ba ma, Malama Ummu-khultum ta faɗa mini cewa bata ji dad'i ba ne, fatan jikin da sauƙi?" "Da sauƙi sosaima Malam Haidar, dan yanzu haka ma suna boko, mun gode sosai-sosai fa, Allah yayi albarka Allah ya taimaka, dama ita Faɗima indai makaranta ce to sai ciwo ke hanata zuwa, shiyasa wancan lokacin ma na je makarantar naku da kai na dan ka zo ka mata faɗa, bata taɓa irin haka ba sai hankalina ya tashi sosai." "To Allah ya kiyaye na gaba Umma, Allah ƙara mata lafiya Alfarman Annabi SAW." "Sallallahu Alaihi Wasallam, Ameen Malam Haidar, ga shi kun yi saɓani bata nan" faɗin Mami tana murmushi dan ta jima da fahimtan akwai abu tsakanin Banafsha da malaminta. Malam Abbo ƙara duƙar da kai yayi ya ce, "Umma daman wajanku na zo, ita kam mun gama magana da ita." Mami ganin bai sha ruwan ba yana jin kunyanta, sai ta miƙe ta ce, "To ka sha ruwa bari na zo" tana gama faɗa ta shige ɗakinta, tana shiga ta saki murmushi tare da ɗaga hannu sama ta ce, "Allah ka tabbatar mana da alkairi." Malam Abbo Mami na tafiya, ya buɗe ruwa ya kwankwaɗa dan kada ta ce ya ƙi sha, kuma saboda ya samu ƙwarin guiwan faɗa mata komai, yana zaune ba jimawa Mami ta dawo ta samu waje ta zauna, sannu da fitowa ya mata ta amsa. Mami ta ce, "yauwa Malam Haidar ina sauraranka." Malam Abbo ƙasa yayi da kansa cikin kunya ya labartawa Mami yanda suka yi da Banafsha, duk abinda ya kamata ya faɗa mata ya faɗa, kansa a ƙasa sosai ya ɗaura da cewa, "Umma ki yi haƙuri, amma ni ina son Faɗima a ko yaya take, amma ta dage da faɗa mini ba za ta yi aure ba, dan Allah Umma a taimaka mini a saka mana baki." Murmushi Mami tayi, wanda kana ganinsa kasan na tsantsan farinciki ne da take ciki, hamdala take kawai a zuciyanta, abinda take hasashen ya tabbata, kuma tasan in Allah ya yarda Banafsha ta samu miji wanda zai nusar da ita duniya da lahira, tana kan murmushin ta ce, "Masha Allah! Tunaninka na ka zo da kanka ka same ni yayi sosai Malam Aliyu, kuma ba komai Insha Allah zan yi magana da ita Faɗima ɗin, sannan ka yi haƙuri da abubuwan da ta faɗa maka, Faɗima ta girma ne kawai amma babu wayo, yaranta har yanzu yana damunta sai a hankali, in Allah ya yarda in har ita rabonka ce to za ka sameta." Malam Abbo ya kasa ɓoye farincikinsa, shi daman ya sani indai ya yiwa Umma magana, to Insha Allahu in ba dai akwai wanda aka bawa ita ba ne, to zai sameta, cikin farin ciki ya ce, "Nagode! Nagode! Nagode! Umma, Allah ya ƙara girma, Allah ya saka da alheri Umma, Allah ya ja kwana ya ƙara girma, Allah ya saka muku da aljanna mafificiya, in Allah ya yarda zan yi wa manyana magana, daman ina son idan muka dai-daita ne ba wani ja'inja a ciki sai na sanar musu." Mami ta ce, "shikkenan ba mastala, zan yi waa wanda za ku nema auran nata a wajansa magana, duk abinda ake ciki za ta faɗa maka, kar ka damu, Insha Allah Faɗima matarka ce." Malam Abbo saboda farinciki ji yake kaman ya tashi ya sha juyinsa a gaban Mami, amma kunyan surkarsa yake, sai dai dole ya ɗebowa Sayyada Roohinsa shoki akan wannan abun murna da farin cikin. Malam Abbo sallama ya yi wa Mami ya tashi ya fice q palourn, ba abinda yake yi sai aikin washe baki, kana ganinsa kasan yana cikin farin ciki, kaman wanda aka ce masa anɗaura an kai masa Banafsha ɗakinsa. Banafsha na ƙoƙarin shiga gidan, shi kuma Malam Abbo na ƙoƙarin fitowa, saura kaɗan su yi karo ya masta da sauri yana faɗin, "subhanallah! Sayyadata afuwa." Ni kuwa baya nayi ban shiga cikin gidan ba, sai da na kalli ƙofan gidan su Umaima da gefen ido, na tabbatar Ya Danish na wajan kuma da alama idanuwansa a kai na suke, murmushi na sakarwa Malam Abbo na ce, "Ba komai Sayyadi." Malam Abbo ƙara washe baki yayi ya fito gaba-ɗaya ya ce, "Sannu da dawowa Sayyadata, a je a huta nima bari na wuce gida daman na zo gaishe da Umma ne." Murmushi na kuma yi na rausayar da kai na ce, "To nima a gaishe mini da su Umma." Murmushi tayi cikin nisto a kogin ƙaunar Banafsha ya ce, "Za su ji" yana faɗa ya wuce yana sakin murmushi. Ni kuwa sai da na kuma satan kallon ya Danish, sannan na ja staki na taɓe baki na shige gida da sallama. Ya Danish tunda suka yi magana da Abbaa shikkenan ya kasa gane wa tunaninsa, yarinyar da yake da burin aure yanzu haka kawai ta fice masa a rai, tun da Abbaa ya masa magana in har zai yi tunanin matan aure to Banafsha ke faɗo masa a rai, ko weekend ɗin da bai zo last ba ma abinda ya hana shi zuwa kenan, zuciyansa ke dage masa akan tana son kallon Banafsha, amma shi sai yana yaƙi da hakan, wannan karon ya kasa haƙura shiyasa da sassafe ya baro Camaroon, dan isowansa bai jima ba aka yi sallahn juma'a, kuma tun da yayi sallahn la'asar yake zaune a ƙofa, zaman jiran yaushe su Banafsha za su dawo, a kan idonsa Malam Abbo ya shiga gidan su Banafsha, da yake kuma ya ganesa, tun da ya ga shigansa sai haushi ya rufe sa. Haka dawowan su Banafsha ma a kan idonsa, tun da ya kalleta kuma ya ji wani irin yanayi mai kama da nustuwa ya lulluɓesa, kaman jinjirin da ya wuni bai samu nono ba sai yanzu, haka ya ji da ya ganta, duk da haka kokuwa yake da zuciyansa yana son ya ƙalubalanci wannan abun da yake ji a kan ta, amma bai tabbatar da ba zai iya hana zuciyansa wannan tunanin ba sai da ya ga murmushin da take yiwa wani daban ba shi ba, ji yayi ina ma shi take yi wa wannan murmushim. Ya Danish kaman ya kamo Malam Abbo ya shaƙesa haka yake ji, har ya wuce abinsa, ajiyan zuciya Ya Danish ya sauƙe, a fili ya furta, "Allah kar ka ɗaura mini son yarinyar nan, ni da kai na nasan na ci mata mutunci, Allah idan ka jarrabeni da soyayyanta nasan wahala zan sha, Allah ka hanani son ta, ka sa ba son ta nake yi ba." Ya IB da isowansa kenan, da mamaki yake kallon Danish ya ce, "Kai kuma tun ɗazu kana ta sumbatu kai kaɗai lafiya kuwa? Wacece ta taɓo ka haka da kake wannan addu'an Allah ya sa kada ka so ta, wacece za ta zarar mana da kai." Hararan Ya IB yayi ya ce, "kai dai da son gulma kake kaman wani mace." Murmushi Ya IB yayi ya ce, "Idan ta yi stami za mu ji, kuma dai in baka da labari ka sani yau, gulma ya jima da kauracewa mata ya koma kan maza, dan mata yanzu ba sa raya sa da kyau, gulma sai maza alaji je majalisa ka ga yanda ake baza hajar mutane kaman shinkafa da kaza a tire, Allah kyauta kawai, yanzu ma kamata yayi ace sheɗan ya fara storon maza ba iya mata ba." Danish abinda ya damesa shi ne damuwansa, ko ta maganan Ya IB ba ya yi. Banafsha na shiga gida ta samu Mami na ɗage ruwan da ta kawo wa Malam Abbo, ganin Banafsha sai ta murmusa tare da amsa sallaman ta ce, "ƴammatan Mami an dawo." Jinjina kai na nayi, ina murmushi na amsawa tare da gaishe da Mami, ta amsa, sai na ce, "Yanzu na haɗu da Malam Abbo ma a ƙofa." "Eh! Daman nima nayi tunanin kun haɗu a waje ai" faɗin Mami tana zama. "Mami wai gaishe ki ya zo yi in ji sa, haka ne?" Na faɗa ina rausayar da kai. Mami dafe goshi tayi ta ce, "Allah shiryaki Banafsha, ki bari idan kin huta sai ki zo ki mini wannan tambayan, tun da shi da ya faɗa miki ba ki yarda ba." Tura baki nayi na wuce ɗakina, ni dai jikina bai bani gaishe da Mami kaɗai ya zo yi ba, addu'a nake Allah ya sa ba maganana ya mata ba, kuma ko maganan nawa ne to ba zan yi aure ba inhar Mamina bata yi ba. *** Ba zan baku haƙuri na rashin yawan page ba, saboda rashin sharhinku ya sa na yi sa kaɗan, ku ma ku ji idan da daɗi 😁 # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE ƳAR KARUWA update group fan's, kowa da kowa uwar batoorl na ƙamnarku. اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 71 _ 75 Sai da na wasta ruwa nayi sallah sannan na fito, samun Mami nayi tana zaune har yanzu, abinci ta saka ni na ɗibo na ci, har na ci na gama shiru Mami bata ce mini komai ba. Washe-gari asabar sai da muka shirya muka je tahfiz sannan da muka dawo muka wuce College, yau class ɗaya kawai muke da shi, dan haka da wuri muka dawo, duk da mun ji ka-ce-na-ce akan za'a manna result ranan, Umaima ta ce mu jira, ni ko na ce bata isa ba gida za mu dawo, haka ta biyoni muka nemi mashine muka nufo gida. Muna tafiya a mashine na ce, "Masoyiya ban faɗa miki yanda muka yi da Malam Abbo ba." Umaima hararana tayi ta ce, "Daman ai iya gudun ruwanki na staya gani, za ki faɗa mini ne, ko har yanzu bata yi stami ba balle na ji." Murmushi nayi na ce, "faɗa miki ai kinsan dole ne, ni bana miki ɓoyel-ɓoyel....." Nan na kwashe duk yanda muka yi da Malam Abbo na faɗa mata. Umaima murmushi kawai ta yi ita ma, ta ce, "Yanzu haka kika ce masa masoyiya?" Ɗaga kai nayi na ce, "eh ai gaskiya ce, ni ba maganan aure a gabana, haka kawai za'a aure ni a dinga faɗa mini magana ko miji ko ƴan uwansa, to ba zan ma fara ba, daman aka ce da gabar na bayar gwanda gabar na hana." Murmushi Umaima ta kuma yi ta ce, "To Allah ya kyauta, tun da dai bakyajin shawara ta Allah da Manzonsa, to ni ba abinda zan ce, Allah rufa mana asiri kawai, amma dai aure ai abin so ne, kuma mutunci ga ko wacce ƴa mace kema kin sani, to stakani da Allah ma wa ya ƙi ni'imar aure? Ai ko ba dan ci da sha ba kana samu a gidanku, to ko dan John-thomas ai ka yi, indai Allah ya nufa kuma ya kawo miji to aure shi ne rufin asirin ko wacce ɗiya mace, ni wani gulma na ji ma nake son miki ke ma, bansan ko kin ji ba dai." Yau ba mu ce mashine ya kai mu ƙofan gida ba, sauƙa muka yi muna tafiya muna kan hiranmu, cewa nayi, "Gulman menene haka?" Umaima ta ce, "kinsan ashe dukan da Umma ta mini wai har da kishi, tana dukana tana surutu ni bana fahimta da yake na jibgu, sai ranan nake jin Abbaa na magana wai saboda ya ce zai auri Maminmu ne, kuma sai ya aure ta." Ajiyan zuciya na sauƙe dan na tuna abinda Mami ta yi ranan dan na mata wannan maganan, kallon Umaima nayi na ce, "To ke kina goyon bayan auren kuwa? Dan ni gaskiya ina jin ta Ummu kaman dai bai kamata ba, kar ta ce Mamina ta ci amanarta, dan nima na ji gulman." Murmushi Umaima ta yi ta ce, "chaɓ! Ai ba ki sani ba masoyiya, Ummu kam ta amince kuma kaman ma har da shawaranta, nidai wallahi zan so haka, shikkenan mu koma zama gida ɗaya, ba wanda zai hanani zuwa gidan Mami ko miki magana tun da mun zama ƴaran baba ɗaya, kin ga ko aurenmu ma sai Abbaa ya mana tare." Murmushi nayi na ce, "ta kwana gidan sauƙi, Allah taimaka ya tabbatar da alkairi, nima zan dage da damun Mamina ayi ma da wuri kowa ya huta." Dariya muka yi dukkanmu cikin farin ciki muka cigaba da tafiya, yau ma dai kaman jiya a ƙofan gida muka samu Ya Danish a zaune, ba tare da na kallesa ba na yiwa Umaima sallama na juya na wuce gidanmu, Umaima gaishesa ta yi a storace, amma sai ya amsa bakomai kaman bai ganta tare da ni ba, hamdala tayi ta shige gida. Ya Danish ci-gaba yayi da kallona har na ɓacewa ganinsa, sannan ya sauƙe nauyayyan ajiyan zuciya a fili ya ce, "jarabawa kenan, ko iya haka Allah ya saka miki abubuwan da nake miki, tun da ga shi kin hanani sukuni kin hana zuciyata nustuwa." Ni kuwa ina shigewa gidanmu na samu ba kowa a palourn, ina ƙoƙarin shiga ɗakina aka yi sallama, juyawa nayi na amsa jin muryan namiji, wani ɗan matashi ne, a mutunce muka amsa sai na ce, "wa kake nema bawan Allah?" Matashin yana murmushi ya ce, "Ko kece Hajiya Ramla?" Kallonsa nayi da kyau, har zan ce a'a sai na ce,."Eh! ni ce, na faɗa ina murmushi dan kada yayi kokonto. Washe baki matashin yayi ya ce,."Daman layinki aka bani, aka ce kina ji da al'amuran lalura tamu ta maza,. shiyasa na zo" ya faɗa yana murmushi. Murmushi nayi inajin kaman na ɗura masa ashar, amma na haƙura dan naci riban zance, na ce, "To fatan da nauyinka ka zo, ina nufin maganan kuɗi." Matashin murmushi yayi ya ce, "Hajiya dubu goma ce da ni a taimaka mini." Wani irin gululun baƙin ciki ne ya turnuƙe ni, wani irin kallon banza na zabga masa, tare da fara zaginsa tass!tass!, haka na mishi na faɗa masa baƙaƙen maganganu sannan ba shiri ya juya, nima juyawa nayi ciki kaman taƙaici zai hallaka ni. Wucewa ɗakina nayi da haushi kaman ya kashe ni, nasan da yasan ni yarinyarta ne, to da shima ƙira na da sunan da na tsana zai yi, duk wani mai zuwa wajan Mami nasan mai zan masa yanzu, dan insha Allah Mamina aure za ta yi. Abubuwan da zan yi na yi na kwanta, dan haushi ko zuwa gaishe da Mami ban yi ba, balle kuma na kula abinci, baccina nayi ishashshe sai da lokaci ya tafi na tashi, alwala nayi tare da yin sallahn la'asar, fitowa nayi na samu Mami na aikinta, ina tura baki na mata sannu ta amsa. Mami ta ga yanda nayi kicin-kicin da fiska, sanin halin rigima irin nawa sai bata ce mini komai ba tun da bata san abinda ya faru ba, haka ni kuma na gaji dan kai na naje na ɗiba abinci na ci, ina ci Mami ta murmusa ta ce, "yunwa ai ba pendon mutum ba ne ko gwaggonsa." Tura baki nayi ina gamawa na ce, "Mami, ashe Umaima bata da lafiya ne shiyasa bata je makarantar ba, kuma har kwanaki suka yi a asibiti." "Ashsha! Subhanallahi! Allah ya bata lafiya, ai ba mu da labari, in Allah ya yarda zan shiga na duba jikin nata, kwana biyu ma Ummunku bata leƙo ba, tun da ta zo ta duba jikinki" faɗin Mami tana aikinta. "Ameeen Mamina, yauwa Mami mun ji labarin wai za'a manna mana result, a taya mu da addu'a Mami Allah sa mu ga alkairi, daman Alhaji ya ce zai mini kyauta ma" na faɗa ina murmushi dan jira nake kawai ya tambayi abin da nake so, ni kuma na faɗa masa abinda na jima da ƙudurcewa a rai na. Mami ta ce, "To Allah ya sa ku ga alkairi, mu kuma Allah sa mu ji alkairi, Alhaji kam yana can wata ƙasar ma ai." Tura baki nayi na ce, "Ai dai zai dawo Mami, kuma nasan zai mini kyauta na." Murmushi Mami tayi ta ce, "To Allah dawo da shi lafiya." Da, "Ameen na amsa." Hira muka dinga yi da Mamina, amma ko sau ɗaya bata ambato Malam Abbo ba, balle na ji ko ya faɗa mata wani abun, ganin haka sai na share lamarin nima, sai da na taya Mami aiki sannan na shirya tafiya makarantar yamma. Ɓangaren Ya Danish dai aiki ya kallesa, bai ankare ba sai ga shi wankin hula na neman kai sa dare, yanzu gaba-ɗaya baya da aikin da ya wuce zama a waje yana jiran ganin giftawan Banafsha, ga shi tun zuwansa bata je ko ƙofan gidan su ba balle kuma a kai ga ta shiga, shi abin ma damunsa yake yi, ga shi Abbaa ya tuna masa saura musu sati biyu su kawo mata su yake jira ko ya aura musu ko ma wacece, Umma tun zuwansa ta bi sa da maganan tun da yana da budurwa yayi magana sai a tura, ko kuma ya koma Camaroon ya dubo a cikin yaran yayyunta ko akwai wacce ta masa, amma nan ma Danish yayi shiru abinsa, shi damuwansa kawai rashin sukunin da zuciyansa ke ciki game da Banafsha. Umaima ta fito a gida ta samu Ya Danish zaune a ƙofan gida, ganinsa sai ba ta yi gigin ko bin hanyan gidan su Banafsha ba, duk da bata kalli ta fito ba, ta juya za ta tafi sai ya ƙira ta, juyowa Umaima ta yi ta ce, "Ga ni yaya." Ya Danish ya ce, "Ita mara kunyar ƙawar taki ba za ta je makaranta ba ne?" Umaima dai a storace ta ce, "Nima ban sani ba yaya." Staki Danish yayi, ya buɗe baki zai yi wani maganan sai ga Banafsha ta fito, a ɓoye kada Umaima ta gane ya sauƙe ajiyan zuciya tare da cewa, "To sai ki tashi ku tafi ai tun da ba kya ji, kuma ki tabbatar kin kula sosai." Umaima miƙewa tayi a storace ta bar wajan, suna tafiya da Banafsha ta sauƙe ajiyan zuciya ta ce, "Masoyiya ba za ki ce mini sannu ba." Taɓe baki nayi na ce, "akan me?" Hararana Umaima tayi ta ce, "Ba ki ga ya Danish da ya stayar da ni bane, wai tambayana ya ke ba za ki je bane, na ce su ya Danish an fara dawowa hanya, ya fara gane Annabi ya kafu, yanzu zan samu peace of mind, dan yanzu ya zama miskilin dole ma." Kafaɗa na ɗage irin ko a jikina ɗin nan, na ce, "shi ya jiyo " daga haka ban kuma cewa komai ba, har muka isa muka yi karatunmu muka dawo. Mun dawo ma a ƙofa muka samu Ya Danish, nan kowa ya kama hanyan gidan su. Da dare muna zaune muna kallo da Mamina sai ta dube ni ta ce, "Faɗima." Hankalina na kan kallo na ce, "na'am Mami." "Ina son ki bani hankalinki, za mu yi magana mai muhimmanci." Ɗauke idanuwana akan TV nayi, na ce, "Ina sauraranki Mamina." Gyaɗa kai tayi ba ko alaman murmushi a fiskanta ta ce, "Ina son ki faɗa mini ya kuka yi da malaminki, da ya faɗa miki tasa maganan ke me kika faɗa masa?" Ni tun da naga Mami bata mini maganan Malam Abbo ba, tun jiya sai na mance da kashinsa ma, amma jin tambayan da ta mini yanzu sai na cunna baki na ce, "Ni ba abinda na ce masa." Ƙara tamke fiska Mami tayi ta ce, "Kinsan bana wasa da ke ko? To maza ina sauraranki faɗa mini abinda na tambayeki." Tura baki nayi cikin shagwaɓa na ce, "cewa yayi yana so na zai aure ni" ina faɗan haka sai nayi shiru. "Da ya faɗa miki hakan, sai ke kuma kika ce masa me?" Mami ta tambaya tana jefa mini mugun kallo. Kaman zan yi kuka na ce, "Mami Allah gaskiya na faɗa masa, ya ce yana so na zai aure ni, sai ni kuma na faɗa masa gaskiya ba aure zan yi ba, ai gaskiya ce Mami, ni ba zan yi aure ba, tun yanzu ana mayar da ni saniyar ware akan jarabawan da Allah ya mini, idan nayi aure dangin miji da miji su dinga gallazawa rayuwata kenan su ma.." Wani mugun stawan da Mami ta buga mini, shi ya sanya ni yin shiru na haɗiye sauran maganata, cikin tsawa ta ce, "Idan ba ki yi aure ba dan ƙaniyanki me za ki yi? Banafsha ki fita a idona na rufe, kada ki bari rai na ya ɓaci fa zan saɓa miki, idan ba ki yi auren ba so kike na saka ki a gaba kaman television ina kallonki ko kuwa na kwaɗaki a tire kaman kwaɗo na cinye? To ki mai da hankalinki." Tura baki nayi, ciki-ciki na ce, "Ni dai ba auren da zan yi, haka kawai a dinga ce mini ƴar mace, a ce mini ƴar karuwa, ni rayuwata gaba-ɗaya ba wani farin ciki kenan." Mami ta ce, "Banafsha kinsan Allah zan saɓa miki a kan wannan maganan, ke baki san cewa Allah ma da kansa yana tausayawa duk budurwa ko saurayin da suka mutu ba aure, kuma sun kai yin auren ba, idan ba ki yi auren ba me za ki yi? Me damuwanki da maganan mutane? Banason shashanci da rashin hankalinkin nan." Tura baki nayi na ce, "Ni dai ba wani auren da zan yi, aka masta mini kuma shikkenan sai na shiga duniya, daman gado ba karambani ba." Ranƙwashi Mami ta mini mai kyau ma kuwa, sannan ta ce, "To zan gani cikinmu wa ya isa da wani, tun da har kin yi girman da ina faɗa kina faɗa, kuma ki tabbatar Inshà Allah tun yanzu za ki fara shirin aure, muddin ya ce yanzu za'a yi auren, to ko bokon ma stayar da ita za'a yi, aure zan miki." Kuka kawai na saka ina bubbuga ƙafa, cewa nake, "nidai ba auren da zan yi sai an kai ni wajan dangin babana, su za su aurar da ni, kawai in ana so naji magana nayi biyayya a kai ni wajan dangin babana, ai ba'a jikin bishiya aka ɓanɓaro ni ba, nidai dangin babana." Mami ikon Allah ta staya gani, saboda Banafsha dagewa tayi ita sai dangin babanta za'a kai ta sannan ya yarda ta yi aure, numfasawa Mami tayi ta ce, "Banafsha ko kina so ko bakya so za ki yi aure Insha Allah, indai ni ce mahaifiyarki kuma na isa da ke, dangin ubanki kuma kibar maganansu idan ba haka ba zan saɓa miki, zan yi shawara da wanda ya kamata a je neman aurenki wajansa, ke kuma ki saurari Malam Aliyu, idan ba haka ba ni da ke ne, sai na niƙa ki a gidan nan." Tura baki nayi na ce, "nidai ko dole za'a mini to a haɗa ni da dangin ubana tukunna, sai an mini abinda nake so sai na yarda, kuma idan ba haka ba sai dai ke ma Mami ki yi haƙuri ki yi abinda kike so nayi." Mami wani kallo ta aika mini da shi ta ce, "tashi ki bani waje kamun na karyaki, ai kin girma yanzu wuyanki ya kai yanka, duk maganan da kike so faɗa mini kike yi." Miƙewa nayi sumui-sumui na wuce ɗakina, ina shiga na saki murmushi, domin ni ko kaɗan maganan auren Malam Abbo ba baƙin ciki ba ne gare ni, maganan auren Malam Abbo alkairi ne gare ni, domin da wannan batu zan yi ƙoƙari wajan gani lamuran Mamina sun saitu, alhamdulillahi! Daman Allah subhanahu wata'ala ya ce, FA'INNA MA'AL USRI YUSRAH, duk wani tsanani na tare da sauƙi, to yanzu ina ganin na fara tinkaro stanin sauƙi da kuma farin ciki na rayuwata, a haka ina zancen-zuci ina murmushi ban ankare ba, har ɓarawon bacci yayi gaba da ni. Washegari Lahadi muka je makaranta safe da yamma duka tare da Umaima muka dawo, kuma duk ya Danish na nan yana kallonmu bai ce mata komai ba, ni kuma ko gigin shiga gidan su ban yi ba dan bana ko ƙaunar kallonsa balle haɗa inuwa da shi, stakanina da Mamina kuma bata ƙara mini maganan Malam Abbo ba, illa iyaka da ta ce mini na sauraresa. Wannan karon Ya Danish bai koma ba har sai washegari Litinin, a hakan ma wai dan Umma tana surutun bata gane ma abinda ke damunsa shiyasa ya shirya zai koma, dai-dai lokacin da muka fito tafiya College shi ma ya fito, ni da Umaima tafiyanmu muka yi za ku nemi mashine, amma sai ya tsaya a gabanmu ba tare da ya juyo ya kalle mu ba ya ce, "ku shigo." Kallon sama da ƙasa na yi wa motar sannan na kawar da kai, Umaima jin ya ƙara magana sai ta riƙo hannuna ta ce, "masoyiya ki yi haƙuri mu shiga ya sauƙe mu." Hararanta nayi ban ce komai ba, na sake hannunta na yi gaba, Umaima kaman za ta yi kuka, ta kalli Ya Danish ta kalleni, Ya Danish kwallon Umaima yayi tare da yin ƙwafa ya ce, "Sai ku taka da ƙafanku ai" yana gama faɗa yayi gaba da mugun gudu, yana wuce inda nake na ja staki tare da hararansa shi da motan nasa. Umaima da ɗan sauri ta iskoni tana faɗin, "Masoyiya mu godewa Allah yanzu ya sha nistojin ya daina bala'i, idan ba haka ba ai da tuni ya shuka mana, ke ma me ya sa za ki ƙi shiga?" Hararan Umaima nayi na ce, "banason magana ki ƙyale ni, tun da dai naga ban hanaki shiga ba ke da motan yayanki, aikin banza aikin wofi, kina wani cewa na shiga sai ka ce baki san irin abinda yake mini ba, ko da ya ke ba laifinki ba ne, daman aka ce naka sai naka, ni bare ce stakaninku." Umaima dariya tayi sosai ta ce, "rai na bai ɓaci ba sai ki fama, anji ɗin ke bare ce, mutum sai ka ce kububuwa, rashin kirkin naki yau ni za ki yi wa kenan? To Allah huci zuciyanki." Hararanta nayi na ce, "oho muku ke da yayanki, kuma dan ki ji mun ɓata ma kowa yayi hanyansa." Murmushi Umaima ta yi ta ce, "Daman wallahi kaman kin san zaman lafiyanmu yayi yawa, ana ƙawance ana ɓatawa ya fi daɗi da ƙargo, amma kullum ni baki haƙuri, ke kuma yin haƙuri, ya kamata ai ko casuwa mu dinga yi, ko da yake ai ma Ummu ta ce mun yi dambe da muke yara, amma ni nake saka ki kuka." Dariya maganan Umaima ya bani, dan haka na dara muka tari mashine muka wuce makarantar, muna zuwa muka ci karo da kyakkyawan labari, an manna dodon bango, Umaima ta damu mu je mu gani, amma na ce ta bari ba yanzu ba, tasan yanda muke ƴan sturut ɗin nan sai a maste mu ko a cika mana ciki da warin hammata, ga kuma wani na stamin zafin da ake yi. Sai da aka tashi sannan muka samu ganin result namu, amma duk da haka ba mu muka duba ba, dan duba mana aka yi, alhamdulillahi dukkanmu result yayi kyau yanda ake so Masha Allah. Muna komawa kowa yayi gidansu, da farin ciki na faɗawa Mami, har da ɗagani Mami tayi dan farin ciki, saboda result yayi yanda ake so, sai godiya ga Allah. Haka muka cinye wannan satin ma cikin farin cikin kyawun result namu, sannan a hadda an fara bitan karatun musabaƙan da za mu yi a cikin jimeta da sauran makarantu na local government's ɗin Adamawa State, tsakanina da Malam Abbo kuwa yanzu ina sauraransa amma dai bana sake jiki da shi sosai, dan har yanzu ina kan bakana kar abu ta kwaɓe gaba ya ce na cutar da zuciyarsa ko kuma na yaudaresa, akwai abu guda da ke burgeni da Malam Abbo, sam-sam a makaranta baya nuna ma akwai wani alaƙa na daban stakaninmu, Malami da ɗalibarsa kaman baya haka muke, kuma ba ya zuwa zance sai ranan Lahadi ko kuma Alhamis, da yake ba mu zuwa makaranta ran Alhamis, sam-sam ba ya takura mini, tun da ba ni da waya, ta nan ɓangaren ma ba ya takura mini. Tun da na fara sauraran Malam Abbo, sai kuma wani shaƙuwan ta shiga tsakanimu, mastayinsa da kiman da nake basa kullum ƙaruwa yake yi, Malam Abbo ya iya soyayya yan da ko wacce mace za ta buƙata, kuma yana ƙoƙarin mini nasiha da tunatar da ni rayuwa, alhamdulillahi sai fatan alkairi stakaninmu. Har aka cinye wannan hutun ƙarshen makon Ya Danish bai zo weekend ba, muka shiga wani satin wanda a wannan weekend ɗin wa'adin da Abbaa ya ba su zai cika, da kuma wa'adin da ya bai wa Mamina na ta yi tunani, har juma'a ta yi ba Ya Danish ba alamansa, dan haka Abbaa waya ya ɗaga ya ƙirasa, sai da ya sollesa tass sannan ya faɗa masa ya zo ko ransa yayi mugun ɓacuwa, ba shiri ya Danish ya shirya ya kamo hanyan zuwa. Da ya ke Umaima ta yi zazzaɓi kwana biyu, sai Mami ta shirya da yamma bayan an yi la'asar ta shiga gidan su Ummu, da sallama ta shigo gidan, ta samu Ummu zaune a palour tare da Ya Farooq, cikin fara'a ya Farooq ya gaishe da Mami ta amsa, sannan suka gaisa da Ummu, tana murmushi ta ce, "Mamin yara sai yau aka samu daman leƙo gidan namu." Murmushi Mami ma tayi ta ce, "ai gidan naku ne yana neman fin ƙarfin shiga na, yanzu ma dai yarinyata na zo dubawa da jiki shiyasa." Dariya Ummu ta yi ta ce, "Mu da muke addu'an a shigo din-din-din, ina wanda ya isa ya ce ba za ki shigo ba." Yaƙe kawai Mami tayi ta ce, "Ina yarinyar tawa?" Ummu ta ce, "ai Umaima ta ji sauƙi Mamin yara, ina ga tana sallah ne ma, da yanzu kin gan ta..." Ummu bata gama rufe baki ba sai ga Umaima ta fito tana murmushi, ta buɗe baki ta ce, "Mamina ayoyoo, sannu da shigowa..." Umaima bata gama magana ba, ta stinkayo muryan Umma na faɗin, "kika ƙara faɗan wani kalma ran ki zai ɓaci, wuce ki koma ciki, shashashan yarinya kawai. Daga Ummu har Mami da Ya Farooq duk da kallo suka bi Umma, Umaima rau-rau ta yi da idanuwanta kaman za ta yi kuka, wani kallon Umma ta jefe ta da shi ta ce, "koma ciki na ce." Umaima juyawa tayi ta koma ciki, Ya Farooq dai da mamaki yake kallon Umma, ƙarshe tashuwa yayi ya fice dan baison ganin abin kunya. Mami murmushi tayi kaman ba komai ta ce, "Umma Kabeer barka da yamma, ya jikin Umaiman?" Wani irin kallon banza, kallon stana Umma ya jefawa Mami tare da sakin dogon tsaki ta ce, "Munafuka kawai, wato kin biyo mu har gida ki ƙwace mijin namu, amma tun da yake ke ɗin ƴar bariki ce dole ki lauye da duba yarinyata, to ba'a buƙatan gaisuwan an yafe miki, tashi ki fice mana a gida, ƴar ƙwace kawai." Mami murmushi ta kuma yi ta miƙe tare da kallon Ummu ta ce, "Ummun su sai anjimanku, Allah ƙara sauƙi." Ummu nauyayyan ajiyan zuciya ta sauƙe ta ce, "ki yi haƙuri Mamin yara, ke kuma Maman Kabeer gaskiya abin da kike yi bai kamata ba." Umma a hasale ta hayayyaƙo wa Ummu ta ce, "To babbar munafuka algunguma, an faɗa miki duk abinda ke faruwa ban sani ba ne? Wallahi can ya ƙare miki a maste-mastinki, ƙarya kike a auro wata balle ki samu daman haɗe kai da wata a gidan nan." Murmushi Ummu ta yi ta girgiza kai tare da cewa, "shi dai kishi ba hauka ba ne, dan haka kisan me ke fita a bakinki, kada ki ga ina miki shiru, ba storonki nake ji ba, gudun tashin hankali nake yi, kuma Insha Allah sai ya aurota." Umma na ƙoƙarin yin magana sai Mami ta yi saurin taran numfashinta ta ce, "Dan Allah kuyi haƙuri dukanku, in Allah ya yarda ma ba abin da zai haɗa ni da mijinku balle wannan tashin hankali ta faru, kuma ni ban shigo dan haɗa ku faɗa ba, dubiya na zo yi kuma na yi zan tafi Allah ƙara sauki" Mami na gama magana ta juya ta fice a gidan, cikin damuwa, ita ko ta rasa mijin aure me ya kai ta haɗa hanya da Umma, balle har su haɗa miji, ita auren da ma gaba-ɗaya babu shi a lissafinta. Umma kuwa da harara ta bi Mami da shi har ya fice a gidan, sannan ta juyo ga Ummu ta ja staki tare da cewa, "aikin banza aikin wofi, kuma wallahi dan ki ji ba gwaninta kika yi ba, tunda abin ba ni kaɗai ta shafa ba, miji nawa ne kuma naki." Ummu murmushi tayi ba tare da ta tankawa Umma ba ta shige ɗakinta, tana koɗa halin kishi irin na Umma. Mamina ko da ta koma gida, ɓoye damuwanta ta yi, ban ga alama ba kuma bata sanar da ni ba, ɓangaren su Ummu ma ba wanda ya yiwa Abbaa maganan abin da ya faru, Umaima dai ba yanda ta iya da halin Umma, ko mene mahaifiya ce dole ta ji magananta. Washegari asabar sai ga ya Danish da sassafe, sai da Abbaa ya dawo sannan suka zauna shi da Ya Danish, Ya Farooq da kuma babban yaya. Abbaa ne ya fara magana ya ce, "Farooq da Danish na baku lokaci, kuma ga shi lokacin kun cinye sa murƙus, ba wanda ya bani amsa mai kyau a cikinku, hukuncin nawa kuke so na zartar ko?" Danish ƙasa yayi da kansa yana sosa ƙeya, shi kuma Farooq murmushi yayi, sai yaya babba ya ce, "A yi haƙuri a ƙara musu lokaci Abbaa, kasan yanzun lamarin daga matan har mazan sai a hankali." Wani kallo Abbaa ya yiwa yaya babba ya ce, "To ubana ba zan ƙara musu lokaci ba, kai da kake da mata yanzu baka jin ka cika mutum, baka jin wani nustuwa ta daban? Ai duk namijin da ya kai riƙe mata muka ba shi da ita, to ba'a niste yake ba, kawai a gansa haka ne a ƙyalesa, an faɗa maka gauranci daɗi ne da ita? Balle kuma ga wanda ke ƙoƙarin ƙewata ƴar mutane mutunci, to ba lokacin da zan ƙara musu, ko su fidda mata aje a tambayo musu ko kuwa ni da kai na nayi musu matan, idan ma idanuwansu sun makance ne, to nawa a buɗe suke tarr! Ai duk cikinsu ba wanda zai ce ba shi da budurwa, to ba za'a yaudari yaran mutane da ni ba dan haka kun ji me na faɗa ai, babu ɗaga ƙafa." Ya Farooq ƙasa yayi da kai ya ce, "Abbaa ni dai ina jira ne daman ka ƙira mu, amma mun gama magana da wacce nake nema, iyayenta kuma sun ce na turo manyana daman." Jinjina kai Abbaa yayi ya ce,"To ka taimaki kan ka, inba haka ba kuwa za ka ga yanda ake yiwa namiji auren dole, to kai kuma Malam Danish ina sauraranka ya muke ciki? Ka samu ne ko na bada sadakanka?" Daga Abbaa da yayi maganan, har su yaya babba ba wanda maganan bai sa dariya ba, ya Danish sosa ƙeya yayi ya ce, "Abbaa nima dai na ba da kai na sadaka wa wata." "To Masha Allah! Duk Allah ya muku albarka, kun taimaki kan ku" Abbaa ya faɗa yana murmushi. Yaya babba ya ce, "To sai ku faɗa mana yaran gidan waye ne, dan a shirya maganan zuwa magana da iyayensu." Ya Farooq ya ce, "Sunanta Ruƙayya gidansu na anguwan Kaban." Abbaa jinjina kai yayi ya ce, "Madalla! Allah tabbatar da alkairi, kai kuma Danish fa." Danish sosa kai ya fara yi, yana in-ina, "uhmñ...umn..am..dama...daman ba..am Abbaa dama dai ni ba wai mun dai-daita da ita ba ne, izini za'a nema mini tukunna." Kallonsa Abbaa yayi ya ce, "To malam Danish, masu bin starin addini yanda ya kamata, hakan ma yayi ai Allah muku albarka, wacece, in ya so gobe ko jibi sai a tambayo maka." Danish ƙasa yayi da kai ya ce, "am Faɗima ce, ina...ina..ina nufin Banafsha." Ba iya Abbaa ke kallon Danish da mamaki ba, hatta ya Farooq da babban yaya kallon mamaki suke bin Danish da shi, gani suke dai kaman bai san abinda yake faɗa ba, kamun Abbaa yayi magana tuni yaya babba ya ce, "Amma dai Danish baka san sunan wa ka ƙira ba ko? Banafsha dai kake nufi ƙawar Umaima, yarinyar Mami?" Abbaa ya ɗaura da cewa, "Banafsha da ka mayar da ita kuran wasanka ƴar gidan amaryan da zan aura Ramla, ita kake nufi ko wata daban?" Maganan Abbaa duk dariya ya basu wai ƴar gidan Amaryan da zai aura, amma suka maste kawai suna sauraran Danish, shi kuma cikin tabbatarwa ya ce, "Ita dai Abbaa, ka yi haƙuri, wlh ita nake so." Jinjina kai Abbaa yayi ya ce, "riƙe haƙurinka idan ka je wajanta zai maka amfani, ni ai mai farin ciki da hakan ne, zan yi addu'an Allah tabbatar da alkairi, Uba ya auri uwa, ɗan sa ya auri yarinya, Masha Allah, in Allah ya yarda zan yi magana da ita idan na je zance." Ya Danish murmushi yayi yana addu'an komai ya zo da sauƙi, shi ya rasa irin Soyayyan Banafsha da ya mara diran mikiya, ya Farooq dai mamaki yake har yanzu, yana kuma tunanin yanda za'a kaya da Umma idan ta ji wannan magana, yaya babba kuma dai kallon Danish bai san abinda yake ba yake masa, saboda ko shi da yake namiji idan aka ce shi ne suka wannan ƴar stama da mutum to ba zai yarda ya so shi ba balle aure, lallai akwai aiki a gaban Danish, haka zaman nasu ya waste bayan sun ɗan tattauna abubuwan da ya kamata. Ya Danish washe-gari da sassafe ya bar gari baya son ma ya haɗa ko ido da Umma, dan yasan idan ta ji labari to akwai yin ta, amma bai da mastala tun da Abbaa ya yarda kuma zai tsaya masa, yanzu a yanda yake ji ba abinda ba zai iya yi ba akan soyayyan Banafsha, Allah-Allah yake a tambayo masa ya fara zuwa ya samu ya kori wannan saurayin nata, shi ana tambayo masa to kusan kullum sai an gansa a Mubi. Ranan Lahadi kaman kullum Malam Abbo ya zo muka sha hiranmu, ya ce zai turo amma na ce masa ya dakata tukunna, haka ya haƙura ba dan ya so ba, Mami ta ƙira mini Alhaji mun gaisa na faɗa masa result na yayi kyau, ya tambayi abinda nake so, amma na ce sai ya dawo, idan ya zo zan faɗa masa, haka muka yi sallama akan ba zai wuce wata guda ba zai dawo, Mamina kuwa ko da ta ƙara mini maganan aure to abin da na faɗa mata ranan shi na maimaita, sai kuma ta koma lallashina ganin na dage. Mun ci-gaba da zuwa makaranta boko da tahfiz tare da Umaima har yau da ta kama Alhamis, da yake ba mu da class da safe, to ba mu je da wuri ba, sai wajan ƙarfe goma muka bar gida muka tafi College. Abbaa ya ƙara wa Mami sati guda akan watan da ya bata, to yau Alhamis ya yanke ranan juma'a zai je wajan Mami, sai ya ce bari ya sanar da su Umma maganan auren Danish dan su san da shi, don abun ya yiwa Abbaa daɗi ko ba komai hakan ma zai ƙara nistar da Umma. Ƙiran Umma da Ummu Abbaa yayi, gyaran murya yayi ya ce, "Sai ku fara shirin da ya kamata, na tarban abokiyar zamanku, da kuma matan yaranku, zan faɗa muku ne na fita haƙƙinku ba wai dan dole ne sai na faɗa muku ba, Farooq ya samo mata a nan anguwan Kaban, sai kuma Danish a nan gida ya samu tasa matar, Faɗima yake so, kun ga abu ya zo gidan sauƙi, tuwo na mai na, ni ina son uwa, yarona kuma yana son yarinyar, dan haka ina gargaɗan ku da yin tashin hankali, Sabeera wancan karon ki daka mini yarinya akan kishinki na hauka, kina ga na zuba miki ido ban ɗau mataki ba, kin ɗauka banza kika daka ba, to zan ɗau mataki, kuma kika yi wannan karon to matakin da zan ɗauka zai baki mamakin da ba ki taɓa zato ba, aure ba gudu ba ja da baya daga ni har Danish Insha Allahu, indai Allah ya nufa to sai mun aure su." Ummu da mamaki take kallon Abbaa, ta ce, "Danish dai ke son Banafsha? Anya ka ji da kyau?" Abbaa jinjina kai kawai yayi bai ce uffan ba. Umma kuwa saboda haushi ma ta kasa cewa komai, miƙewa tayi ta fice, Abbaa kuma taɓe baki yayi bai ko stayar da ita ba, dan yanzu halin Umma ya fara gimsarshi, Ummu kallon Abbaa tayi ta ce, "kana ganin hakan ya dace? Ba za'a ja wa yarinyar nan mastala sosai a rayuwanta ba, a yanzu ma kusan kullum cikin kuka take da damuwa da mahaifiyarta, idan aka mata irin wannan auren kana ga yayi? Ni bana tunanin ma daga ita har mahaifiyarta za su amince da wannan batun, duk da babu wanda yasan abinda ya faru ranan." Abbaa murmushi yayi ya ce, "ke dai ki ce Allah tabbatar da abinda ya ke alkairi." Ajiyan zuciya Ummu ta sauƙe, ta ce, "Ameen summa Ameen." Umma tana shiga gida ta shige ɗakinta, gabas da yamma kudu da arewa ta rasa me za ta yi ta huce, ta rasa wani mataki za ta ɗauka, wai yau Danish da ke goyon bayanta ne ya kwaye mata zani a kasuwa, ya rasa wa zai so sai fistararriyar yarinyar nan, tana fama da Umaima ta raba su, sai kuma shi ya kawo magana mai gaba-ɗaya, maganan aure, to ba zai saɓu ba, dole ta ɗau mummunan mataki, wayanta ta ɗauka ta dannawa layin Danish flashing, saboda cherge's na international call to sai dai ta yi flashing ba daman ƙira. Ya Danish a nasa ɓangaren daman ya jima yana stumayen ƙiran Umma, dan haka yana ganin flashing nata ya biyo ƙiran, Umma na ɗauka bata saurari ko sallaman da yake yi ba ta ce, "Danish ni za ka tozarta? Ni za ka nunawa kai ɗan yau ne? To wallahi idan kaga ka auri yarinyar nan to ko bayan rai na ban amince ba, sai dai ka mutu babu aure." Danish ajiyan zuciya ya sauƙe ya buɗe baki zai yi magana, sai Umma ta dakatar da shi ta ce, "Idan ka kuskura ka ce mini wani abu, to wa billahil Azeem ranka zai ɓaci, kai ka san halina fiye da kowa, to kada ka yarda rai na ya ɓaci..", Umma na gama masifanta ta kashe wayanta tana huci. Haka Umma ta wuni da bala'i da masifa, abin na cin ta kwata-kwata ta kasa haƙuri ta kasa nistuwa, har yamma ta yi ta kasa haƙuri, wani abu ke ingiza ƙeyanta zuwa gidan Mami. Yau har ƙarfe shida ta same mu a makaranta, sai da ta ɗora da mintuna sannan aka tashe mu, muka kamo hanya muka dawo gida, Umaima ta wuce nasu nima na wuce namu gidan. Muna zaune da Mamina bayan sallahn isha'i sai kawai ganin mutum muka yi a kan mu ba ko sallama, daga ni har Mamina da mamaki muke kallon Umma Sabeera, dan nidai a iya sanina ban taɓa ganin ta shigo gidan mu ba. Kamun Mami ta yi wani yunƙurin buɗe baki tayi magana sai gani muka yi Umma Sabeera ta fito da wuƙa, ta yi kan Mamina gadan-gadan, ihu na stala na yi kan Umma ina faɗin, "Me muka miki? Kashe mu za ki yi Umma? Dan Allah ki yi haƙuri." Umma tureni gefe tayi tana faɗin, "Wallahi idan ke mayya ce yau sai na kashe ki kowa ya huta, idan ya so nima a kashe ni, haba dan Allah kin dameni kin addabeni kin staya mini a maƙoshi, abun ya wuce na aure mini miji da za ki yi, ya koma har yarona kuka lashewa zuciya yana son yarinyarki, to indai ina raye ko aure ɗaya ba zai ƙullu ba, wallahi ba za mu haɗa jini da karuwa kuma mayya ba." Mami ƙoƙarin kare kanta take yi, amma Umma ta zuciya sosai, ƙoƙarin caka mata wuƙan take a ƙirji, suna kokowa har dai Allah ya bawa Umma nasaran caka wa Mami wuƙa a ciki, ihun da Mami ta yi shi ya tattaro mini sauran ƙarfin jikina, da kumburarren goshi na mike, na rarumi tire a gefe ba ƙwalawa Umma a kai, faɗuwa ta yi, ga Mami a kwance cikin jini ga kuma Umma a kwance a sume, ihu na kuma saki na fice a gidan da mugun gudu, cikin anguwa na yi ba hijabi ganin ba mutane sai na juya gidan su Umaima, a bakin ƙofa na ci karo da Abbaa da ya fito saboda ihuna da yake jiyowa. Kasa magana nayi sai kawai nuna masa gidanmu nake ina faɗin Mamina, ina kuka, Abbaa bai tsaya tambaya na ba yayi gidanmu, muna shiga ya ga halin da Umma da Mami ke ciki, bai tsaya tambayan ba'a si ba ya fice, tare da ya Sadeeq suka shigo, Mami kawai suka saka a mota, nima Ya Sadeeq ya ja hannuna na shiga muka nufi asibiti, Abbaa ran sa a ɓace ko kallon Umma bai yi ba, General hospital Mubi muka nufa. ⭐⭐ CAS Bunayd suna tafiya yana jan staki ganin irin lokacin da suke ci, tafiya ya ƙi ci ya ƙi cinyewa, har sai bayan isha'i suka shigo mubi, hamdala yayi, sannan aka wuce da shi direct General hospital na mubi. Ayi haƙuri rashin update jiya, jikinne sai a hankali kawai ku ta tayani da addu'a. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE My ƙawas Oum inaya. Nana ƙanwar Soja. Aunty Salma (maman humaira da bashir) اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 Noted: afuwan fan's, mastayin Bunayd na Air Force ba CAS bane, wato Chief of the air staff, mastiyinsa ACM ne, Air Chief Marshal, a yi haƙuri da mistake ɗin, shi CAS a land army ne, ACM ne Air Force, kuma Bunayd Sojan sama ne Air Force kenan, abin ne da rikitarwa sorry for the mistake.👏 🅿️ 76 _ 80 Driver na parking, Bunayd ya fito a rikice, amma idan ka kallesa ka ranste ma rigima yake ba'a cikin damuwa yake ba, amma kuma shi ya san damuwan da yake ciki na abinda ya samu Abeed, cikin hanzari suka shige ciki, sojan da ke tare da Abeed ne ya musu jagora har ɗakin da Abeed ke ciki, ya so shiga amma kuma aka tsayar da shi, sakamakon taimakon gaggawa da ake kan bai wa Abeed ɗin. ACM Bunayd stayuwa yayi a bakin ƙofan ya na safa da Marwa, da ya kasa haƙuri sai ya juya kawai, dai-dai lokacin kuma ya samu kuma ana rikici tsakanin Nurses da wata kyakkyawar matashiyar budurwa, da ke rikice kaman wata mara ishashshen hankali, taɓe baki yayi zai fice sai idanuwansa suka sauƙa akan mara lafiyan da ke kwance a gadon ɗaukan marassa lafiya, ɓata rai yayi ya nufe su gadan-gadan. Banafsha tun barowansu gida kuka take yi, Abbaa saboda ɓacin rai ko magana ya kasa yi, sai ya Sadeeq ne ke ƙoƙarin bata baki akan tayi haƙuri, amma ta ƙi shiru har suka isa General hospital ɗin. Abbaa kuma layin babban yaya ya ƙira, yana ɗauka Abbaa bai tsaya amsa sallaman da yake masa ba ya ce, "kabeeru ka je gidan Mamin Banafsha ka ɗau uwarku, kuma kar ka kuskura ka shigar mini da ita gidana, idan ƙafanta ya taka gidana ko gawanta ne, to ban yafe maka ba, kuma kuna farfaɗo da ita ta kwana cikin shiri dan ƴan sanda suna hanya." Babban yaya cikin tashin hankali ya miƙe, daman yana wajan aikinsa ne, gareji yake yi, cewa yayi, "Abbaa me ya faru? Me ya kai Umma gidan Mami?" Guntun tsaki Abbaa ya ja, ya ce, "kana tambayana ne, ni na san irin haukan da ke damun uwarku, to dai ka ji abinda na ce, mu yanzu haka ma muna general hospital", Abbaa bai jira me babban yaya zai ƙara faɗa ba, kawai ya kashe wayansa yana yin ƙwafa kawai. kusan tare motan su Abbaa suka iso da su Bunayd, Bunayd suna shigewa, su Abbaa kuma cikin gaggawa aka ɗauko gadon ɗaukan mara lafiya aka ɗaura Mami a kai, suna shiga ciki Nurse ɗin ta dube su ta ce, "kunsan ba'a attending irin waɗannan patient's ɗin sai da police ko?" Abbaa ya ce, "Ku yi haƙuri ku fara ceton rayuwanta baiwar Allah, police kam dama dole ne ku gan su, dole su shigo cikin lamarin nan." Ya Sadeeq dialing layin Ya Farooq yayi amma ba ya shiga, dan ya Farooq ma a general hospital ɗin yake aiki, Banafsha cikin shessheƙa ta ce, "Dan Allah dan Annabi ku taimaka ku fara bata agajin gaggawa tukunna, ai an ce muku police ɗin za su zo." Magiyan duniya su Banafsha sun yi, amma amsa guda Nurses ɗin ke basu, ba'a amsan irin wannan mastalan ba tare da police ba, domin yan da mace-mace ke yawa ana ɗaure likitoci basu ji ba kuma ba su gani ba to dole sai da shedan police, dan ko ma mene ya biyo baya to dai ba za'a ga laifin likita ba balle har a ɗaure sa, Abbaa ransa ne yayi mugun ɓaci, dan haka ya sa Ya Sadeeq ya dubo musu wani likita abokin ya Farooq, Abbaa kuma ya ɗau waya ya ƙira babban yaya ya kuma faɗa masa ya turo musu police tukunna. Banafsha fa ta ƙulu ta kai wuya cikin karaji da masifa ta fara balbala bala'i, cewa take, "Amma dai wallahi ku kam an yi marassa imani, marassa tausayi, asararru kawai, daman dan uban me kuka yi karatun naku, kuma aka baku daman aiki a asibiti, gomnati ta gina asibiti kuma ta ɗauke ku aiki, take biyanku albashi, ba duk dan al'umma ba? To in Allah ya yarda Mamina ba abinda zai sameta, shegu, munafukai, marassa imani, ƴan uwan fir'auna kawai, kuma nima zan zama likitan nan, aka kawo mamanku duk ni da kai na zan ƙarisa su...." masifa kawai Banafsha ke yi, kaman wacce aka aiko daga sama, Abbaa sai tausanta yake amma ta ƙi yin shiru, kuma a dai-dai lokacin Bunayd da ya ga duk abinda ke faruwa, ya iso wajan rai a ɓace. ACM Bunayd ko kallon inda Banafsha ke masifanta bai yi ba ya kalli Abbaa, a ɗan daƙile ya ce, "sorry Sir! Za'a dubata yanzu." Shi da kansa ya tura gadon Mami, sai sauran sojojin suka zo da gudu suka amshi gadon suka tura, likitan da ke duba Abeed ne ya fito, ganin su da wata patient ɗin, take ya saka aka kai ta ɗakin ba da agajin gaggawa ba tare da ya tambaya ba ko ya ce wani abu. Abbaa kaman zai rungume Bunayd ya ce, "Allah maka albarka likita, mun gode, Allah saka da alkairi ya rufa asiri duniya da lahira, idan ana samun irinku a likitoci ai ba wanda zai mutu saboda irin haka, sai dai in lokacinsa ne yayi, Mun gode bawan Allah" Abbaa ya faɗa dan duk ɗaukan sa Bunayd irin likitoci masu taimako da tausayin nan ne. Bunayd murmushin da ko leɓensa bai kai ba yayi ya ce, "Ba komai Sir, your welcome." Banafsha tun da aka yi gaba da gadon da Maminta ke kai sai ta kuma ƙaro sabon walaƙanci, duban Nurses ɗin ta yi ta ce, "Munafukan Allah to ahirr ɗin ku za'a duba Mamina, kuma ba ɗan banzan police ɗin da za mu ƙira balle kuma Soja, ƴan baƙin ciki kawai, so suke na zama marainiya gaba da baya ba uwa ba uba, to ta Allah ba ta ku ba..." Masifanta ta ci gaba da yi har ta ƙarisa wajan su Abbaa. Duk abin da Banafsha ke faɗa a kunnen Bunayd yana ji, surutun nata bai dame sa ba tun da ya saba da na ƙannensa, amma maganganun nata ma dariya yake basa, kallo ɗaya ya mata ya kawar da kai kaman bai kalleta ba yana yastina fiska, ba tare da ta masa godiya ba ta wuce su ta ƙarisa ƙofan ɗakin da ta ga an shigar da Maminta, bata hango kowa a ciki ba sai Maminta, juyawa ta yi kuma kaman za ta yi kuka ta ce, "Abbaa ka ga mugaye, su ma ba dan Allah suka karɓe ta ba, ga shi sun ajiye ta ita kaɗai, so suke ta mutu, wayyoo ba'a ƙaunata ana son Mamina ta mutu." Abbaa ƙarisowa yayi wajanta ya ce, "ki yi shiru Faɗima, wannan likita mai mutuncin ya sa za'a dubata kin ji." Banafsha kwaɓe fiska ta yi ta ce, "tun da dai ba zai duba Mamina da kan sa ba, to ba shi da wani mutunci shi ma, shi ɗin banza, to ya duba ta da kansa mana indai da gaske yake yana da imani kuma shi na gari ne ba kaman sauran ba, ni wallahi ba za'a yaudareni a banza ba a bar uwata ta mutu ba, aikin banza daga shi har sauran har Umma duk in Mamina ta mutu sai na yi Shari'a da su, ko kuma na bi rana na kashe su, bin dare ma ai storo ce, ni da ranan Allah ido na kallon ido zan ƙaddamar musu." Tana rufe baki sai ga likita ya iso wajan da sauri, bai shiga ɗakin da Mami ke ciki ba ya wuce inda zai kai sa ɗakin da Abeed ya ke, da sauri Bunayd ya stayar da shi, cikin turanci ya masa magana akan tun da sun yi aikin Abeed ɗin su duba matar mana kada a rasa ta. Likita duban Bunayd yayi ya ce, "sorry Oga, an mata abinda ya kamata, raunin nata ba sosai bane, idan muka gama da shi za'a dubata." Kamun Bunayd ya buɗe bakin ba da amsa, tuni Banafsha ta diro a gaban likita idanuwanta rufe ta ce, "wallahi ƙarya kake, maƙaryacin likitan da bai san aikinsa ba, wuƙa aka yage Mamina da shi, kuma ka ce raunin ba sosai ba ne, kai kasan jinin da ya fita a jikinta ne ma, wa ma ya sani ko har kayan cikinta sun yanyanke, to nima ɗalibar malaman lafiya ce, ina College kuma ina last year, dan haka kada ka wani faɗa mana ƙarya mun san me ne a aikin muka, kuma ba inda za ka tafi idan ba ka shiga ɗakin da aka kwantar da Mamina ka duba ta ba." Daga likita har Bunayd baki suka sake suna kallon ikon Allah, ganin yanda budurwan ta dage da masifa iya ƙarfinta, likitan ya kasa haƙuri sai da ya dara ya ce, "To masifaffiyar likita, tun da kinsan komai kuma kin kusa gama College sai mu baki kayan aiki ki duba Momin taki ko." Banafsha sai kuma ta shagwaɓe ta ce, "dan Allah duba Mamina ka ƙyale wancan ɗin, ai shi ma ka duba sa, ka koyo adalci mana likita, ai in ba ka practicing to ba za ka iya riƙe mata biyu ba, kawai Mami ma s dubata tun da shi ma an duba sa." Bunayd bai kalli Banafsha ba, amma yana sauraranta, ji yake kaman ya kwanta a ƙasa ya ta dariya har cikinsa yayi ciwo, wai ai ta kusa gama College ita ma likita ce, murmushi yayi har sai da haƙoransa suka bayyana, sannan ya kuma magana da turanci ya ce, "ka turo wani likitan ya duba ta, please a yi a gama da Captain namu dan transfer muke so a mana zuwa Kano." Banafsha ma ta ƙi kallon Bunayd, likitan take kallo ta ce, "wallahi ban yarda ba, ni kai ka mini, kai nake so ka duba Mamina, wani likitan ya je ya duba Captain ɗin nasu, tun da ba mu na Captain namu bane, ni Mamina ce Captain tawa." Bunayd murmushi ya kuma yi tare da yi wa likitan magana da ido, sai ya juya wajan Abbaa da yayi poster yana ganin ikon Allah, Abbaa bai taɓa sanin haka Banafsha take ba sai yau, Bunayd murmushi yayi ya ce, "ina so za mu yi magana Sir." Abbaa gefe suna yi da Bunayd, ya ce, "Ina sauraranka likita." Bunayd kiston kan sa ya shafa ya ce, "Sir ni ba likita ba ne, ni Soja ne, muma mun kawo wani ɗan uwanmu ne ya samu hatsari." Abbaa baki ya buɗe ya ce, "Ai ko na ji, amma dai kai a sojojin ma daban kake, ai ko likitoci ka fi su imani da tausayi, Allah kuma ya basa lafiya, ka yi haƙuri da shirmen Faɗima, ba haka take ba kawai abinda ya samu mahaifiyarta ne ya rikita ta haka." Bunayd cewa yayi, "Ba komai..", zai yi magana sai ƙira ya shigo wayan Abbaa, haƙuri Abbaa ya bai wa Bunayd sannan yayi picking, "ina cikin asibitin kuna ta ina?" Faɗin Abbaa da ke kare da waya a kunnensa. Yaya babba ya ce, "Abba ka fito bamu san a ciki ta ina ba." Abbaa ya ce, "To ganinan", yana faɗa ya kashe wayansa, sannan ya dubi Bunayd ya ce, "bawan Allah bari na zo, Yarona ya taho da polisawan ne." Bunayd gyaɗa kai kawai yayi ya juya wajan likitan. Likita dan dolensa sai da ya shiga ɗakin da Mami ke kwance, sannan ya fito ya tafi ɗakin da Abeed ya ke, jaraban masifan Banafsha dariya ma yake basa, sai ya ji ta burgesa. Bunayd bayan ya je office na likitan, bayani ya masa dangane da Abeed, akan sun yi duk abin da ya kamata, gobe ma za su iya ɗaukan sa su tafi Kano ɗin, harbin bai yi muni sosai ba a cinya ne kuma an cire alburushin, sai su ƙarisa jinyan a asibitin Kano, dan zai fi samun kulawa sosai ma, Bunayd hamdala yayi, sannan ya ce, "likita wannan matar fa?" Murmushi likitan yayi ya ce, "Ni da farko na ɗauka ma ai duk tafiyanku guda, sai da masifaffiyar likita ta yi bayani" likita ya faɗa yana murmushi. Bunayd murmushi shi ma yayi dan ya tuna kalaman Faɗima, kaman yan da ya ji sunanta a bakin dattijon ɗazu, cewa yayi, "likita, ita ya nata condition ɗin? Komai zai tafi dai-dai a nan ko ita ma a sanja mata asibiti, ko da a cikin Yola ne." Murmushi likitan yayi ya ce, "a'a Oga, ita matar fa kaman yan da na faɗa raunin nata da sauƙi, anyi niyan caka mata wuƙan a ƙirji ne, amma sai ya kauce ya kar ci cikinta, bai ma shiga sosai ba, sai dai daman abin da ya sa muke so a ce sun zo da police saboda maganin samun mastala ne, ya kamata wanda ya mata haka a hukunta sa, dan gaskiya kasheta aka yi niyan yi, amma aka bar ta a nan asibitin ma komai zai tafi dai-dai, in Allah ya yarda za mu yi iya bakin ƙoƙarinmu muyi duk abinda ya kamata." Bunayd gyaɗa kai yayi ya ce, "good, Allah bata lafiya" yana gama magana ya sallami likitan ya fita, lokacin dare ta yi sosai-sosai. Abbaa ma bayani ya yi wa polisawan, suka samu likitan shi ma ya musu bayani, sannan ya faɗa musu Soja ne ya shiga lamarin shiyasa ya amshe ta ma, samun Bunayd suka yi, cikin girmamawa suka gode masa, amma Bunayd gyaɗa musu kai kawai yayi bai ko kallesu ba, sannan a gadarance ya ce, "Ku tabbatar kun mata duk wani hukunci yan da ya kamata dai-dai, she attempt to commit a murder, dan haka idan na ji ba'a mata hukuncin da ya kamata ba, ku ne za ku yi facing na hukuncin" yana gama magana ya miƙe ya yi gaba. Polisawan amsawa suka yi, sannan suka tafi, tare da yaya babba da Abbaa suka koma aka ɗau Umma da ta farka zuwa lokacin da mugun ciwon kai, daman tana gidan yaya babba ne, tana kallon su ta miƙe tana muzurai, Abbaa staki kawai ya ja, ya ce, "ki je na sake ki, kuma aure ki sani ba gudu ba ja da baya, ke kin fita a banza, ita kuma za ta shigo hankali kwance." Umma za ta yi magana, polisawa suka tisa ƙeyarta sun ƙi bata daman magana, yaya babba gaba-ɗaya yasan Umma bata kyauta ba, abin bai masa daɗi ba, amma dai uwa-uwa ce, sai ya ji ba daɗi sosai, har ya ji haushin Danish dan shi ya ja komai, ya stani yarinya kuma ya dawo ya ce yana son ta, bayan shi ya ƙara ingiza Umma har ta musu mugun stana, yanzu ga shi abinda ya faru." Abbaa gida ya koma, ya faɗa wa Ummu abin da ke faruwa, Ummu hankalinta yayi mugun tashi, Abbaa ya ƙira ya Sadeeq akan ya dawo da Banafsha gida, tun da dare ta yi, kuma ana kula da Mami, ya Sadeeq ya amsa. Banafsha na tsugunne gaban ɗakin da Mami take, sai ga ya Sadeeq, yana zuwa ya ce, "sistor ki zo mu je gida ko, zuwa safiya sai mu dawo." Tura baki Banafsha ta yi ta ce, "Ni dai ina nan da Mamina ba in da zan je." Ya Sadeeq yayi-yayi ta ƙi, dan haka dan dole ya ƙyaleta, dan ko da ya faɗawa Abbaa ma cewa yayi a ƙyale ta. Bunayd ma an yi da shi ya koma hotel tun da Abeed ɗin na huta wa, amma ya ce yana nan kawai, ba dan sojojin sun so ba, haka suka mara masa baya kwanan asibiti ya same su. Bunayd shi ba kwanciya zai yi ba, dan haka zama yayi kawai a ɗakin da Abeed ɗin ya ke, idan ya gaji kuma ya tashi ya fito. Banafsha kuma likita ya faɗa mata ta shiga ciki ta kwanta, tun da daman Mami ita kaɗai ce a ɗakin, yau Banafsha ta ga daren da bata taɓa gani ba a rayuwanta, don kuwa baccin ma gaba ɗaya ta kasa, ya ƙauracewa idanuwanta, haka ta dinga juyi, ƙarshe alwala ta ɗauro ta ta da sallah, sai da ta yi nafilfiulunta sannan ta miƙe ta fito. Mutumin da Banafsha ta gani a tsaye shi ya storitata, za ta koma ciki sai ta jiyo daddaɗan muryansa na faɗin, "storita kika yi?" Banafsha tana jin muryan ta gane mai yin turanci ɗazu ne, tura baki tayi ta ƙarisa fitowa ta zauna, Bunayd ma ya ƙariso wajan ya zauna ba tare da rata sosai stakaninsu ba, wayansa ya fidda yana lastawa ya ce, "scared girl." Cunna baki ta kuma yi ta ce, "Ni ba mastoraciya ba ce, ni bana storon kowa sai Allah, sai na yi kokawa da aljani ma lafiya lau, duk wanda ya mini rashin kirki nima masa zan yi ba storo." Taɓe baki Bunayd yayi ya ce, "Kuma kina gani aka yi wa Mom naki wannan abun ba ki ɗau mataki ba, ashe kina da kirki." Banafsha da ta tuno abinda Umma ta yi, ai a masifance ta ce, "wallahi na buga mata abu a kai ita ma sai da ta suma, sam-sam ban da kirki ban san shi ba, bani da mutunci idan aka mini rashin mutunci, ni sai na stigewa mutum gashin mugun waje ma ba ruwana." Murmushin gefen baki Bunayd yayi, bai kuma cewa komai ba ya ci gaba da danna wayansa, Banafsha sai mita take ita ɗaya, da ya gaji sai ta ɗago ta leƙa fiskan Bunayd, zaro idanuwa Banafsha tayi tana faɗin, "Mutum ko aljan", a ranta, ganin irin kyawun Bunayd. Bunayd a jikinsa ya ji tana ƙare masa kallo, yastine fiska yayi kaman wanda ke yi wa General shagwaɓa, ya ce, "Bana son kallo da yawa." Banafsha banza ta yi da shi, tana ta satan kallonsa, ita ba ta shiga harkan maza, amma dai wannan ta kasa ɗaure masa fiska ma, ga shi kyakkyawa kaman Malam Abbonta. Bunayd haɗe fiska yayi a zuciyansa ya furta, "wannan yarinya ta ci sa'an condition da nake ciki, if not da ita ma ta amshi nata rabon na abinda nake yi wa masu mini kallon ƙurilla, da masu taɓa ni babu sadaki" yana gama magana a zuciyansa ya ja guntun tsaki tare da miƙewa ya shige ɗakin da Abeed ya ke. Banafsha taɓe baki tayi, ta ce, "Allah kai mu safiya za ka san ni ka ja wa tsaki", tana gama faɗa ita ma ta miƙe ta shige ɗakin da Mami take, tana kwanciya kuma ba jimawa bacci yayi gaba da ita, a ɓangaren ACM Bunayd kuwa idanuwansa biyu haka ya kwana, dan ƙarshe ma alwala ya ɗaura yana ta nafilfiulunsa har asuba ta yi. Su Umma a police station, tun cikin dare aka mata statement da komai na attempt to commit murder, da yake tana cikin haushi har lokacin tuni ta amsa musu ita ta yi kuma da saninta ta yi, duk da dai ta amsa amma ta jibgu, kamun aka bar ta sai gari ya waye. Abbaa yan da ya ga safe haka ya ga dare, gaba-ɗaya abun ya damesa ba kaɗan ba, shi ji yake sakin da ya yi wa Umma bai wadatar ba, da ace ya sani da ya haɗa mata Juni da majina tukunna, ƙwafa kawai ya kwana yi, Ummu ta ba sa baki amma ya ƙi sauraranta ma, dan ko da ta nuna a bar maganan auren banafsha da Danish, Abbaa kaman zai dake ta haka ya hayayyaƙo mata, dole taja baki ta yi shiru tana faɗin Allah ya huci zuciyansa. Umaima tun da ta ji labari hankalinta ya tashi, kwana ta yi tana kuka har ciwon kai mai stanani ya rufe ta, tausayin Banafsha da haushin halin Umma su suka dame ta, gaba-ɗaya ji take ina ma ana sanja uwa da wallahi sai ta sanja nata uwar, ita sai yanzu ma take ganin ƙoƙari da tawakkali irin na Banafsha, ashe haka ake ji idan mahaifiyar mutum na aikata ba dai-dai ba, ji take kaman ta kashe kanta ta huta, sai ɓarawon bacci ne ya samu nasaran yin gaba da ita, washe-gari kuma ko ta kan magana makaranta bata bi ba, tana taya Ummu aiki, ta shirya ita ma za ta je asibitin. Abbaa da Ummu da Umaima suka kama hanyan asibiti, aka bar gida ba kowa, dan Nana bealkysou ta fi zama a gidan yaya babba ita kam yawanci, tana taya Hindatu aiki saboda cikin jikinta da ya girma. Yaya babba sammako yayi a police station amma an ƙi barinsa ya kalli Umma, tun da ta amsa laifin ta shikkenan aka killace ta, dan gudun kada ta yi yunƙurin kashe wasu ma, yanzu haka ma shirye-shiryen kai ta prison suke kamun a fara shari'anta a yanke mata hukunci. Ya Danish da yake can bai san wainar da ake toyawa ba, babu wanda ya ƙira sa, babban yaya na fushi, Abbaa kuma ba ya son ya sanar da shi dan kada ya ce ya fasa, saboda yanzu yan da Abbaa yake ji ko Danish ya fasa, muddim yarinyar ta amince to sai ya aureta ko zai mutu, dan yafi son ya nunawa Umma bata ita ba. Da sassafe Bunayd ya sa aka yi arranging na komai yanda ya kamata dan da wuri yake son su wuce, amma so yake kamun ya tafi ya bar wa Faɗima rabonta, na kallon ƙurillan da ta masa jiya, shi ka'idansa ne, mace ba za ta kula stabgansa ba dai-dai da ƙwayan zarra. Banafsha kuwa saboda ba ta yi bacci da wuri ba, sai da ta makara, gari yayi haske fayau ta tashi, lokacin shida da rabi ta yi ma, a gurguje tayi alwala ta yi sallah, azkar nata da komai, tana idarwa kuma su Umaima suka shigo, Umaima ƙarisawa tayi jikin Banafsha ta ce, "Dan Allah Masoyiya ki yi haƙuri, ni ma ban ji daɗin abinda Umma ta yi ba, amma tun da tana hannun hukuma da sauƙi, Allah bai wa Maminmu lafiya." Hawayen da ya zubo wa Banafsha ta share, tare da amsawa da Ameen, gaishe da Abbaa ta yi ya amsa cikin tausayinta, Ummu ma sai ɓoye nata hawayen ta yi, sannan ta amsa gaisuwan Banafsha ta ce, "zo ki ɗiba abinci ki ci ko yarinyar Maminta." Banafsha ɗan Murmushin yaƙe ta yi kawai, ta ce ba yanzu ba, suna zaune cikin jimami har sai wajan ƙarfe tara na safe sannan ta karya, bayan ta cika cikinta ta ja hannun Umaima suka fice a ɗakin. Umaima dai bin Banafsha tayi har ta ga sun nufi wani ɗaki, dai-dai za su shiga sai ga likita nan ya fito ga Bunayd a bayansa, shi likitan yana kallon Banafsha sai ya murmusa ya ce, "good morning annoying doctor." Banafsha murmushi ta saki tare da amsawa, Umaima ma suka gaisa da likitan da fara'a. Bunayd da ke bayan likitan, haɗe fiskansa yayi ya fidda wayarsa yana lastawa, Banafsha a yanayin rashin kirki ta ce, "Sannunka bawan Allah ya mai jiki?" Banza da ita Bunayd yayi bai ce komai ba, ta kuma magana shiru bai ko ɗago ya kalleta ba, sai da ta yi na uku sannan ya ɗago rai a haɗe ya wasta mata kallon banza ya ja guntun tsaki, Banafsha idan ran ta yayi million to ya ɓaci, saboda masifa har vibrating take yi, Umaima na gefe na ganin ikon Allah ita da likita. Banafsha a hasale ta ja staki ta ce, "aikin banza aikin wofi, dan ma ka ci albarkacin Allah da Manzonsa ana maka sannu ai da ko kallo ba ka ishe mu ba, Allah ne ya ce, yana farin ciki da kuma kyautan aljanna ga duk wan da idan ya haɗu da mutum zai yi gaggawan masa magana cikin aminci, kuma Annabi SAW ya ce mai zuwa gaishe da mara lafiya yana hanyan aljanna, dan haka ka ji duk ba dan kai na yi ba, kuma daga yau ka ji, ko na ganka a hanya na kula ka, to ba nice Faɗima ba, aikin banza kawai kana nuna kai ba na gari ba, to wani ya faɗa maka shi ma nagari ne ko yana da kirki, ni ɗin nan na fika iya rashin kirki da wulaƙanci ka gode wa Allah ma na kulaka." Umaima da mamaki take kallon Banafsha, take kuma maste dariyanta, Bunayd dai ko ɗagowa bai yi ba balle yasan da halittanta a wajan, abun ya kuma ƙara damun banafsha, dan haka a masife ta kalli likitan ta ce, "Kai kuma da ya ke ba za ka iya riƙe mata biyu ba, kai ba adali ba ne, shi ne har za ka fara zuwa duba mara lafiyansa ba za ka duba Mamina ba tukunna ka ji storon Allah." Likita maste dariyansa yayi ya ce, "Allah ya so ma mata ta ɗaya ce kuma ba kishiya zan mata ba, dan haka shi ya ce a zo a duba masa ɗan uwansa, ke kuma ba ki faɗa a zo a duba miki Maminki ba." Masifa Banafsha ta fara, ka ranste gaskiya ne da ita, Banafsha akwai ƙarfin hali da samun waje, dan ko ita da kanta mamakin abinda take tun da ta zo asibitin nan take. Bunayd jin surutun nata yayi yawa ɗagowa yayi a gadarance ya ce, "Idiotttt!"" Yana faɗan haka ya juya ya koma ɗakin da Abeed yake, yana mai jin haushinta, dan kawai ya sake mata shi ne take son rena sa, tana ƙoƙarin haɗa kan ta da shi, mastalan yara kenan musamman mata, guntun tsaki ya ja, ya yi dialing na wani layi, da turanci yayi magana akan sun gama a zo a ɗauke su. Likita kuma gaba yayi yana dariya, su Banafsha na bin sa a baya, Banafsha sai ƙarewa Bunayd tanadi take yi, ga shi ko sunansa bata sani ba, amma ta ce sunansa ba zai wuce Isa stoho ba ta sani, haka suna je likitan ya gaisa da su Abbaa sannan ya duba Mami, sai da ya gama sannan ya ce, Abbaa ya biyo sa office nasa, yana gama faɗa ya fice. Abbaa ya ce, "Ni ko na ce, Faɗima ina labarin wannan soja mai mutuncin, ya nasa mara lafiyan?" Taɓe baki Banafsha tayi ta ce, "Au! Wai daman Soja ne? Shiyasa mana yake jin wulaƙanci, bai san gidan rashin kirki ya zo ba, yana can da halinsa nai wari da muni ba kaman fiskansa ba." Umaima dariya ta fashe da shi ta ce, "Amma ki dinga jin tsoron Allah Banafsha, kina abu kaman wani ke ce da gaskiya, ko da ya ke samun waje ne yake damunki, irin wannan masifa haka, waɗanda ya kamata ki musu ba ki musu ba sai wan da ba ruwansa." Banafsha hararan Umaima ta yi, Ummu ta tambayi ba'a si, Umaima ta labarta mata, ita Ummu ma duk da damuwan da ke damunta sai da ta murmusa ta ce, "Allah shiryaki Banafsha." Abbaa ya ce, "Ai bansan yarinyar nan ta iya rikici ba sai jiya, gaba-ɗaya kaman an kunnata" ya faɗa yana dariya ya fice a ɗakin ya nufi office na likitan. ACM Bunayd kuwa ba jimawa mota ya zo ya ɗauke su, bayan an saka Abeed a bayan motan, dan ya farka, amma an masa alluran bacci, haka suka yi gaba, sun sha tafiya kamun suka isa jimeta, suna zuwa dama already an gama komai, suka hau jirgi kuma sai Kanawan dabo, tumbin Giwa ko da me ka zo an fi ka. Abbaa bayan likitan ya basa izinin shiga, sai yayi sallama sannan ya shiga, ya zauna a inda likitan ya nuna masa, ƙara gaisawa suka yi. Likita numfasawa yayi ya ce, "am Alhaji, jikin Mami da sauƙi dan wuƙan bai wani shiga jikinta ba, yankanta yayi kaɗan kawai, to storitan da ta yi ne, shi ya jefata cikin wannan suman, duk da dai akwai allurorin da aka mata ne, amma da ta farka tun cikin dare, amma Insha Allah zuwa anjima za ta iya farkawa, kuma ba zai wuce kwanaki zuwa sati guda ba Insha Allah komai zai zama dai-dai." Abbaa murmushi yayi jin likitan ya ce Mami, dan yana da tabbacin a bakin Faɗima ya ji, hamdala yayi da dai jikin Mamin ba wani muni yayi ba, sannan ya ce, "Mun gode sosai likita, Allah saka da alheri, Allah ya ƙara muku ƙarfin zuciyan taimakon bayin Allah." Likitan murmushi yayi ya ce, "Ba komai Alhaji, a gode wa Allah da kuma wannan bawan Allahn na Soja, sannan kuma ku dai tabbatar kun yi abinda ya dace, domin kasheta wanda ya soka mata wuƙan yayi niya, kawai dai Allah ya taƙaita ne." Abbaa ajiyan zuciya kawai ya sauƙe, dan idan ya tuna ji yake kaman ya je ya kashe Umma shi ma ya huta, cewa yayi, "in Allah ya yarda za'a yi abinda ya dace, dan ma tana hannun hukuma, shi kuma wannan bawan Allah Sojan Allah ya masa albarka ya saka masa, yanzu ya maganan receipt na abubuwan da za mu biya, kamun a sallamemu." Murmushi likitan yayi ya ce, "Ai kar ku damu Alhaji, dan Soja ya biya komai da komai daga nan har ku tafi, ko wata guda za ku yi ba mastala, balle ma Insha Allahu bama fatan ta kai sati guda." Abbaa ji yake kaman yaya dan farin ciki, cewa yayi, "Shikkenan likita mun gode, a taya mu gode masa, yanzu bari naje na gode masa, daman ba mu haɗu ba tun da na zo." Likitan cewa yayi, "Ai kuma Alhaji bana tunanin yana nan zuwa yanzu, dan sun riga da sun karɓi transfer na abokin nasu zuwa Kano, yanzu haka ma wataƙila sun fita a Mubi." "Ashsha! To Allah saka masa a duk inda yake, Allah kuma ya stare sa da alkairinsa" Abbaa ya faɗa, tare da miƙewa, suka yi musabaha da likitan ya fice. Abbaa yana komawa ɗakin ya ce, "Faɗima kin ji ikon Allah, wannan soja mai mutuncin har da kuɗin jinyan Maminku ya biya, gaskiya wannan Soja da kyakkyawan zuciya yake, Allah masa albarka." Ummu ta amsa da, "Ameen! Idan yana da mata Allah ƙara musu zaman lafiya ya kuma albarkaci zuri'ansu, idan kuma bai da ita, Allah basa ta gari."(Hhhhh na ce Ummu da Bunayd na kusa da kin sha mamaki dan wannan mugun addu'a kika masa🤣) Banafsha a zuciyanta sosai ta ji daɗi ta kuma godewa Allah ta gode masa, a fili kuma ta ce, "Abbaa, wallahi ba wani na gari bane fa shi ɗin, bai da wani mutunci balle kirki, ai Umaima tana kallon abinda ya mana ɗazu." Umaima saurin girgiza kai tayi ta ce, "Haram! Ba da ni za'a yi wa bawan Allah sharri ba, ki faɗa gaskiya ke ce kika wani dage kaman shi sa'anki, dan haka komai yayi ke kika nema." Hararan Umaima Banafsha ta yi ta ce...... *** A yi haƙuri da typing errors ba editing. MASU SHARHI UWAR BATOORL NA MUGUN ƘAMNARKU, INA MIƘO GODIYA MUTANEN AMANA. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKU NE Hafsat Umar Ɓingel kabi Masoyiya bealkysou Habiba muhammad Yusuf اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 81 _ 85 Banafsha hararan Umaima tayi ta ce, "Anji ɗin." Abbaa ba jimawa ya fita ya tafi wajan aikinsa, tun da ga Ummu da yaranta a kan Mamin, bayan tafiyan Abbaa sai Ummu ta ce su je gida su ma, amma bata musu maganan boko ba dan ta san ba yarda za su yi, su je ba. Da ƙyar Banafsha ta yarda, amma tana tura baki, haka suka fice suka tafi, saboda haushi ma ko duba Bunayd bata yi ba, ta bari akan sai sun dawo ta duba sa, dan bata san da ya tafi ba, so take ta rama idiot ɗin da ya ce mata ɗazu, dan ita ta rasa ma gaba-ɗaya mai ya taɓa tunaninta da ta yi behaving haka, ko me ya kai ta shiga stabgan sa ma oho ta rasa. Suna komawa suka fara zuwa gidan su Umaima, sai da suka gyara gidan, sannan suka tafi gidan Mami, nan ma gyarawa suka yi ko ina ya ɗau ƙamshi, suka ɗaura girki, bayan sun gama suka ci nasu, suka saka na kai wa asibiti, sannan suka saka wa Abbaa suka kai masa gida. Wanka Umaima ta fara shiga, sai da ta fito sannan Banafsha ma shiga, shiryawa suka yi cikin kayan su iri ɗaya da Mami ta ɗinka musu ba jimawa. Masha Allah! Kar ku ga kyawun da Banafsha da Umaimatynta suka yi, kaman ka sace su ka gudu, sai da suka gama komai suka yi sallah, lokacin ma har an sauƙo juma'a, sannan suka koma asibitin. A asibiti kuma, bayan tafiyan su Banafsha ba jimawa Mami ta farka, lokacin ana ƙoƙarin shiga sallahn juma'a, Ummu da kanta ta ƙira Nurse, da yake likita ya tafi masallaci dan haka Nurse ɗin tayi abinda ya kamata. Isowan su Banafsha yayi dai-dai da lokacin da likita ma ya iso, tare suka shiga ɗakin, likitan ya duba Mami babu wani mastala, sai ɗan abin da ba za'a rasa ba, Banafsha kaman za ta yi yaya dan farincikin ganin Maminta ta farka, lafiya-lafiya. Umaima da Banafsha duk suka gaishe da Mami ta amsa da kai kawai, likita ya hanata cin abu mai nauyi, dan haka Banafsha gida suka koma suka kuma kawowa Mami abu mai dama-dama wan da za ta iya ci. Bunayd sun isa Kano da wuri wajajen ƙarfe biyu na rana, komai da yake ready sun wuce asibitin da shi, kuma an ƙara yi masa abin da ya kamata, sannan Bunayd ya bar asibitin ya koma gidansa dan shirin zuwa ɗaurin aure. Babban gidansa da ke anguwan Dala GRA ya nufa, gida ne haɗaɗɗe har ya gaji da haɗuwa fan's, wanka yayi da wur-wuri ya shirya cikin manyan kayansa, idan ka kallesa ka ɗauka shi ne angon ma, masallacin da za'a ɗaura auren a can ya nufa, yana zuwa kuwa ana idar da sallah aka gabatar da ɗaurin aure, da yake ya faɗawa iyayen Abeed, kuma su ma sun yi wa iyayen Nusaiba bayani, duk an amince ba komai tun da kowa yasan ƙaddara, balle ma ga soja, kuma yarinya ta ce tana son mijinta a haka. An ɗaura auren CAPTAIN ABEED TASI'U ADAMU & NUSAIBA YAKUBU NASHE akan sadaki Naira dubu ɗari biyu, bayan ɗaurin aure kuma, Bunayd da sauran abokanaye duk suka yi abinda ya kamata. Abeed kuwa a asibiti ana gama ɗaurin aure ya farka, ko da Bunayd ya zo wajansa sai da ya saka shi ya kira masa Amaryansa Nusaiba, Bunayd dariya ya dinga yi wa Abeed ya ce, "stautsayi ta rista da Ango mai jiran Palace, sorry Captain Abeed, amma kai ma ai da nine kai ba zan je wannan aikin ba atou, haka kawai ga shi an maka baƙin cikin yin mopping na Palace from corner to corner, kai gaskiya ma dole kamilarka ta renaka, yo baka goge mata hadda a take ba ai ba wani suna mai daɗi da za'a ƙara maka, kai in kana son ganin asalin soyayya da girma a wajan Amarya to a ranan da aka kai ta, kada ka bari ta kwana lafiya, balle ma ta kai Sunday, a ranan Friday ka sha hidima ka yi disko, ka kwaso shoki, ka yi har da Apro dance duka a Palace, nan za ka ga wani irin ruwan ƙauna, ai ba abinda ke saita mace ka ga ta ji duniya babu ya kai irin Dragon, ka bata blessfull milk ka kwashi gifted water, ni ana fara maganan aure na ko nan da can ba zan je ba, ƙarshe ma General ne zai je ya ɗauro auren a kawo mini Amaryata, yanzu dai dole ku cinye wata guda babu ko romancigin, ai hidiman cherge a Palace ta wuce Friday to duk buge ce, dan a ranar ma ake son ka jefa ƙwallo a raga, za ka ga albarkataccen baby da za'a haifa maka, wanda ya amsa sunan sa ɗan halak, ranan da aka biya sadaki da ɗuminsa aka same shi, tun sadaki bata huce ba ta salafce" Bunayd ya ƙarisa zancen yana dariya kaman ba lafiya ba, kana gani kasan dariyan mugunta ce. Abeed saboda haushi ji yayi ma ya warke, hararan Bunayd yayi ya ce, "ɗan jagaliyan musulmi, bakinka ya sari ɗanyen kashi, in Allah ya yarda zuwa Sunday na warke, wato tun da baka ƙaunata dole ka mini fatan na kai 1 month a kwance, kuma Allah ya kai mu lokacin naka auren, za mu ga ko za ka gujewa abin da Allah ya hukunta" ya ƙarishe maganan tare da yin ƙwafa, dan ko shi a ransa ba haka ya so ba, irin soyayyan da suke da Nusaibarsa, irin burin da suka ci wa wannan rana ai ba haka ba, amma ba yanda mutum ya iya da ƙaddaran Ubangiji. ACM Bunayd dariyansa ya ci gaba da yi, har da wata English music yake na babu hidimar Palace, sai da ya stagaita dariyan ya ce, "Amma ai da sauƙi tun da raunin ba'a Dragon ba ce, kawai dai tun da a cinya ne ba buga harka yan da ya kamata, sai dai a lallaɓa, ka ga fa'idan auren gantalalliya da nake faɗa maka ko, yanzu da ace ba kamila saliha ka aura ba, ai ba ka da mastalan komai tun da Dragon na lafiya, da kana kwance za ta gabatar da hidima ta yi su doro bucci, su gwara-gwara, a gwargwarawa Dragon chergy." Abeed mai da kansa yayi ya kwanta yana cewa, "Sai kuma ka yi ai, ni dai idan ba za ka ƙira mini ita ba, miƙo mini wayana." Bunayd yana murmushi ya miƙa wa Abeed wayansa, bayan ya masa dialing na layin Nusaiba Amarya. Ƙira na shiga, kaman daman Amarya jira take, ɗauka tayi cikin farin ciki da ƙaunar mijinta ta ce, "Alhamdulillahi ala kulli halin na zama mallakin My Captain, sai addu'an Allah ba wa mijina lafiya." Lumshe ido Abeed yayi yana jin wani irin abu, a hankali ya ce, "babyloff am so sorry." Guntun murmushi Nusaiba ta yi ta ce, "sorry for what Captain? Ƙaddara ce, kuma da yardan Allah mun ma cinye ta, Allah baka lafiya, nikam lada kwasha-kwasha, tun yanzu zan fara cika bankin lada na, ana wastewa zan zo nayi jinyan Captain na." Murmushi Abeed yayi ya ce, "Masha Allah! Alhamdulillahi! Na gode wa Allah da ya mallaka mini ke, tun yanzu ma indai aljannarki a ƙasan ƙafata take, to na ɗage miki, lada kam kina kan samu tun da aka ɗaura albarka nake saka miki, saura albarkan bed kawai." Cikin jin kunya Nusaiba ta dinga amsawa Abeed, suka yi wayansu cikin farin ciki, suna gamawa Abeed ko kallon Bunayd da ke masa dariya, ya ƙi yi, gyara kwanciyansa yayi yana tunanin Nusaibarsa, ba dan ciwo ba ai da zuwa yanzu ko ɗan taɓe-tabe haka da ya yi. Bunayd miƙewa yayi ya ce, "Captain kar ka saka ƴar mutane a corner, ka bari ciwonka ya warke, yau da gobe duk ɗaya ne", yana gama magana ya fice. Ƙwafa Abeed yayi ya ce, "ɗan renin hankali, ana sallamana a ranan ba ɗaga ƙafa wallahi, kuma kai ma lokacinka na zuwa zan rama ne ai. ACM Bunayd komawa gidansa yayi ya shirya, daman freind's na su suna gidan sa, suna jira a kai Amarya kamun su wuce, dan dinnern da za'a yi an mayar da shi sai idan Abeed ya warke, sai yayi fixing time ayi, shi yayi arranging na komai, aka ɗau Amarya aka kai ta gidanta, duk wani abun buƙata da za'a yi Bunayd ake tambaya, ya tsaya ciff akan komai, har aka yi aka waste ranan Lahadi. Abeed ya ce Nusaiba ta kwana a gida tukunna ta huta, sai washegari litinin ta zo, amma sam firr ta ƙi yarda, dan haka shiryawa tayi Bunayd ya je ya ɗauko ta ya kawo ta asibitin, kamun isowansu kuma tuni Abeed yayi wanka ya yi sharr abin sa, kaman ba mai jinya ba, da yake ƙafan da sauƙi ma. Bayan sun shigo ɗakin, tuni Abeed ya buɗe hannu wa Amaryansa, Nusaiba sunne kai tayi wai tana kunyan Bunayd, shi kuwa taɓe baki yayi ya ce, "kin yi a iska Amarya, kunyan mara kunya asara ne, yi abunki lokacinki ne, mu idan namu ta zo har da cherger Palace idan ta kama zan yi a gabanku ba ruwana" ya faɗa yana ɗage kafaɗansa, irin ko a jikinsa. Nusaiba Amarya murmushi kawai ta yi, ta koma wajan mijinta ta zauna, amma bata yi hugging nasa ba, Abeed hararan Bunayd yayi ya ce, "Sai a bamu waje ai, kasan yanzu iyali gare ni, ni ba gauro ba." Murmushi Bunayd yayi ya ce, "Ni ba zan ce komai ba, amma dai ka bi a dai-dai, dai-dai kaman mai slow motion, dan wani ciwon baya yake komawa idan aka charger Palace bai warke ba", yana gama magana ya fice kaman ba shi yayi maganan ba. Abeed murmushi kawai yayi, tare da jawo Nusaiba jikinsa, wani irin ajiyan zuciya suka sauƙe a take, nan suka fara kallon juna cikin soyayya, har Nusaiba ta gaji ta kawar da kan ta, kalaman soyayya suka fara ɓari, daga ƙarshe Abeed haɗe bakinsu yayi, yana mata wani irin kiss mai isar da saƙon zuciya zuwa ga masoyi. Sai da suka yi sati guda a asibiti sannan aka sallamesu, kuma kullum Nusaiba tana can, wanka kawai da girki ke kai ta gida, duk da ma Bunayd na yawan musu takeaway, ga kuma wanda ake kawowa daga gidan iyayen Abeed, da nata iyayen, Abeed kullum sai yayi kiss amma bai taɓa wuce kiss ba, yana daurewa ko yayi yunƙurin wuce kiss sai ya fasa, ya ce sai an sallamesi. Ko da aka sallamesu Bunayd hidima bai ƙare ba, shi ya kai su gidan su, ko da Nusaiba ta shige ciki, tsayar da Abeed yayi ya ce, "Abeed ka bi a slow motion fa, serious ciwo bai cika son ana charging ba, ba ta warkewa da wuri." Abeed hararan Bunayd yayi ya ce, "Idan kai ka biyan mini sadaki to sai ka hana", yana faɗa yayi gaba. Bunayd ɗage kafaɗa yayi, ya wuce abinsa yana faɗin, shi ya gama nasa yayi duk abin da ya kamata, idan ya jawo wani abun ma su suka jiyo, amma gefe guda na zuciyarsa na cewa, "faɗa gaskiya ACM ko kai ne ba za ka ƙyale ba, sabuwar Amarya no be play", murmushi kawai yayi ya ci-gaba da driving abin sa, gidan Papi ya nufa ba gidansa ba. Abeed yana shiga gida ya saki hamdala, ganin Nusaiba na gyare-gyare, ƙarisa wa yayi tare da rungumeta ta baya, a hankali ya kai hannayensa kan na shanunta, wani irin gigitaccen ajiyan zuciya ya sauƙe, a hankali ya ce, "My life saver's, babyloff bar aikin nan, ladansa kaɗan ne, muje ki yi mai lada da yawa." Nusaiba ajiyan zuciya ita ma ta sauƙe, ta ce, "My Captain ba ka warke ba fa." Abeed shi kaɗansa a zuciyansa ya ce, "Ashe gaskiyan ACM Bunayd, wato dai har faɗa mini take ban warke ba, ta rena Dragon, shikkenan ai za ta same sa yanzu kuwa", yana gama zancensa a zuciya, ya mata dabara, yana tattaɓeta har ya ja ta suka yi ɗaki, gaba-ɗaya Abeed notin kam sa ya warware. Nusaiba ma abu ya fara kai mata karo, tuni suka fara ƙoƙarin raba kan su da kayan jikinsu, cikin ƙarfin hali Abeed ya haƙura ya ƙyaleta, wanka yayi ya shirya, ita ma ta yi, suka wuni soyayyan su, dare na yi ya ce kuma bai san zancen ba, alwala ya sa ta tayi, suka gabatar da duk wani abu na al'ada, kayan cin su da Bunayd ya turo musu da shi, suka yi haniƙan, sannan fa aka fara zuba soyayya. Abeed sarrafa Nusaiba ya ke yi kaman abinda aka turo sa yi a duniya kenan, tun da Abeed ya fara haukata mata boob's nata, yana gyara musu lissafi, tuni ta fice a nata lissafin, hidima sosai Abeed suke yi, ko ciwon ƙafan ba ya tunawa, sai da ya tabbatar ya gama da ita, sannan a niste ya fara neman hanyarsa bayan addu'an da yayi, wanda Sunna ya tanada domin ma'aurata, ita wannan addu'a kuwa tana stare masu gabatar da Sunna daga sheɗan, sannan idan a wannan lokacin ma an samu ƙaruwa, to Insha Allah wannan yaro zai zama nistastte ba sheɗani ba, mata w ƙoƙarta ko miji baya yi ke ki dage ki dinga yi, duk iya fitanki hayyacinki, idan ma ba'a iya ba ko bismillah ayi ta wadatar, addu'ar na da matuƙar amfani da muhimmanci, addu'an ita ce BISMILLAHI ALLAHUMMAH JANNIBNASH SHAITAN, WA JANNIBISH SHAITANA MA RAZAƘ'NA. Nusaiba ta ji azaba dai-dai gwargwado amma dai ta daure, Abeed gaba-ɗaya ma ya mance duniyar da yake, hidima yayi ba ta kaɗan ba, sai da ya samu nistuwa sannan ya janye jikinsa tare da rungumeta yana lallashinta, bayan sun starkake jiki, ta gasa kan ta, sun gyara wajan kwanciya, sun kwanta, nan ƙafan Abeed ya fara damunsa, wasa gaske zuwa safiya kaman ya yanke ƙafan ya huta dan azaba. Jikin Mami yayo sauƙi sosai, satinsu guda da kwana biyu a asibiti, aka sallamesu, zuwa lokacin kuma DR ARSHAN sun yi sabo da Umaima da Banafsha, Malam Abbo ya zo har asibtin ya duba Mami. Gefen Umma kuwa tana prison a ajieye, tukunna ba'a bi ta kan case nata ba ma, gaba ɗaya a sati guda kawai ta lalace ta fice a hayyacinta, da yake ƙaramar ƴar tasha ce har ta yi nadaman abin da ta aikata, dan ta galabaita. Ya Danish tun da Abbaa ya faɗa masa ba su yi magana da Mami ba tukunna, sai ya fasa zuwa weekend ɗin, yaya babba kuma gani yake kaman Danish da gangan ne bai zo ba, sai bai tuntuɓe sa ba, kuma ko ya ƙira ba ya ɗauka, shi kuma ya Mus'ab daman ba gwanin zuwa gida ba ne, yana can abin sa. Abbaa ganin halin da Mami ke ciki, sai ya ɗaga ƙafa ba yanzu zai sameta da maganan ba, har Mami ta kuma yin sati da dawowa asibiti bai mata maganan ba, zuwa lokacin ta ji sauƙi sosai, su Banafsha sun ci gaba da zuwa makarantansu boko da tahfiz, in da yanzu suke shirin tafiya musabaƙan su, wanda za su gabatar a cikin jimeta tare da sauran makarantun local ɗin Adamawan. MASU SHARHI UWAR BATOORL NA MUGUN ƘAMNARKU, INA MIƘO GODIYA MUTANEN AMANA. # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚 👄'YAR KARUWA👄💅 Officially 𝘽𝙮 Harira Salihu Isah (Uwar batooler) SADAUKARWA NE GARE KI Baby batoorl (my unborn favorite soul) TUKUICI NE GARE KA SIR Abubakar Sadeeq CEO lafazi writer's association (gidan karamci) Da kuma ɗaukacin member's namu. PAGE NAKI NE Heartbeat, ina mai addu'a Alfarman wannan wata ta Ramadan mai ɗimbin albarka, Allah baki lafiya ya sauƙeki ƙalau ukhtynh. اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله SAW 🖤🤍 🅿️ 86 _ 90 Bayan wani lokaci Mami ta warke rass da ita, amma bata yi maganan Umma ba, lissafi kawai take yi da tunani akan rayuwa, musamman maganan Malam Abbo da Banafsha, dan Banafsha ta dage ba za ta yi aure ba sai dai Mami ta yarda ta yi ita ma, ko kuwa ta koma wajan danginta, wannan zaɓi biyu na Banafsha sun damu Mami, domin burin Mami bai wuce aurar da Banafsha ba, akan hakan kuma za ta iya yin komai, sai dai tuno abubuwa da dama na mata kastalanda akan amincewa da abin da yarinyarta take buƙata kamun a ce tayi aure. Yau Abbaa ya shirya abinsa ya je wajan Mami, ba tare da ta nuna wani abu akan akasin da aka samu ba, haka ta tarbesa da fara'a, kuma ko Abbaa ya ji daɗin hakan, sai ya ji ta ƙara kwanta masa a rai sosai, ya ƙara son ta. Cikin nistuwa Mami ta gaishe sa tare da tambayansa Ummu, amsawa yayi yana washe baki. Abbaa cewa yayi, "Da farko dai ina mai baki haƙuri Hajiya Ramla, ina kuma baki haƙuri, dan Allah ki yi haƙuri da abin da ya faru, daman jiran warkewanki ake yi sai a fara shari'a ma, Insha Allah za'a ƙwatar miki ƴancin ki." Murmushi Mami tayi wanda ke ƙara mata kwarjini, sannan makari ga duk wani damuwanta, cewa tayi, "Lah! Ai ba komai Abbaansu, na haƙura wallahi na yafe mata، saboda duk wata mace mai kishin mijinta za ta iya aikata fiye da haka, kuma ƙauna da soyayyar miji ke kawo kishi, duk da dai kishi ba hauka bane, amma da gaskiyanta ni banji haushinta ba ko kaɗan, da ina hayyacina ma ba zan bari abin ya kai ga hukuma ba, ko nine a mastayinta idan ba wai na danne zuciyata ba, to zan aikata abinda ya fi wanda ta aikata, dan sai na haɗa da mijin duka na ƙone su, kawai dai haƙuri ake tun da Allah ya halatta muku, sai dai mu ce Allah bamu ikon fin ƙarfin zuƙatanmu, Allah kuma ya bamu haƙuri da dangana, tun da ko matan Annabi SAW ma sun yi wannan kishin, har sai da ta kai Allah ya sauƙe aya guda a kan su a cikin Suratul Tahrim, dan haka dai ita kishi halitta ce, Sunna ce, ba yan da za'a yi ka guje mata sai ikon Allah, faɗin Manzon Allah SAW ne ma cewan kaicon ma'auratan da basa kishin junansu, tun da dai sai da kishi sannan ake samu a kiyaye wasu dokokin Allah a zaman auren, to kada ka ga laifinta, Allah ya kyauta kawai." Abbaa shi dariya ma Mami ta basa, jin wai idan ita ce sai ta haɗa da mijin, jinjina kai yayi ya ce, "To yanzu dai idan na fahimta, Hajiya Ramla cikin ruwan sanyi take kafa mini sharaɗi, wato na kulle ƙofa daga kan ki, babu ta huɗu kuma ko na ce ta biyu dai." Wani kallon rashin fahimta Mami ta masa ta ce, "Abbaansu ba dai nufinka ka sallami Maman Kabeer ba?' Abbaa jinjina kai kawai yayi ya ce, "Eh! Saboda bana son tashin hankali da rashin haƙuri, Ita Ummu-khultum ai tana da zuciya da nata kishin, amma ta haƙura duk da haka, tun da ƙarin aure Sunna ce, ga kuma yanayin zamani ya zo ƙarshe." Murmushin taƙaici Mami tayi tare da jinjina kai ta ce, "Ai daga wannan kuma ka riga ka faɗi zaɓe Abbaansu, ai yanzu na faɗa maka nima idan ba wai Allah ya taimaka ba zan yi fiye da haka, duk da ba sharaɗi bane amma ai hannunka mai sanda ce, gaskiya Abbaansu ka yi haƙuri kawai ka dawo da matarka, ku cigaba da zamanku lafiya, ni xan fi son hakan, domin yanzu gani zan yi kaman nima aje-aje gaba za ka iya mini haka akan wata, ka yi haƙuri amma zai fi ka dawo da matarka uwar yaranka, da stohon zuma ake magani, kuma da kake maganan Ummu ai kai ma cewa ka yi nata kishin daban, to da haka za ka fahimci kowacce mace da irin nata kishin, ba duka aka zama ɗaya ba, kar garin gudun gara ka faɗa wa zago kuma, a zo ni nafi Maman Kabeer kishi da rashin haƙuri, ka ga ai akwai mastala babba ma sosai." Abbaa murmusawa yayi ya ce, "Ba zan iya dawo da Sabeera ba, saboda idan akan kishi ne kaɗai ta yi hakan, to da sauƙi dan nima nasan kowa da irin halittan kishin da Allah ya masa, amma har da dalilin dan Danish ya ce yana son Faɗima a nema masa izinin nemanta." Da mamaki Mami ke kallon Abbaa, wato dai ranan gaskiya kunnenta suka jiyo mata, daman was-wasi take ko dan storita ne ya sa ta ji kaman Maman Kabeer ta ce, yaronta na son Banafsha, su mayu ne sun lashe mishi zuciya, murmushin yaƙe Mami ta yi ta ce, "Allah ya bawa Maman Kabeer haƙuri, Allah ya huci zuciyanta, in Allah ya yarda tun da bata so, to Banafsha ba za ta auri Danish ba, in ba dai Allah ya rubuta hakan a ƙaddaransu ba, to babu yanda muka iya kuma, sai dai addu'a da fatan alkairi, dan haka wannan ma ba dalili bane da zai sa ka rabu da iyalinka, ka yi haƙuri Abbaan yara, mu mata sai a hankali, haƙuri ake da mu, kaga Allah bai haɗa jininmu da ita ba shiyasa bata son ma ɗan ta ya auri Banafsha, to nan ma ina bayanta, saboda maganin bari kada a soma." Abbaa wani gauron numfashi ya sauƙe cikin ƙara jin haushin Umma akan abin da ta aikata, kallon Mami yayi a yanayi na tausayi ya ce, "Hajiya Ramla a taimaka mana ni da Yarona, gaba-ɗaya tun da aka yi abin nan hankalina ya ƙi kwanciya, sannan yaron nan kwata-kwata ma ya ƙi zuwa ma, balle kuma ya san halin da ake ciki, ya ce sai ya ji labari an yarda ya nemi Fatima sannan zai zo, dan Allah a taimaka mana." Mami ajiyan zuciya ta sauƙe cikin duba lamarin Maman Kabeer, dan ba za ta yarda Banafsha tayi aure a irin wannan gida ba, ita ma babba an yi ƙoƙarin kasheta balle kuma Banafsha yarinya, duk da dai yaron na ƙaunarta(kunsan Mami bata san abin da ke faruwa ba, duka wannan staman stakanin Banafsha da Danish bata da labari), amma ba za ta iya ba, dan haka duban Abbaa ta yi ta ce, "afuwan Abbaan yara, amma magana ta gaskiya Faɗima tana da manemi, wanda zuwa yanzu izini kawai yake jira ya turo manyansa a yi maganan auren su, bai kamata nima duk da ina mace ba, amma na zama mai magana biyu, kuma dai nema cikin nema ko a addinan ce babu kyau." Abbaa kallon Mami yake kaman ya ƙwala ihu, ya ce, "sosaima Hajiya Ramla, nema, cikin nema babu kyau, dan haka in Allah ya yarda zan yi ƙoƙari na basa haƙuri ya nemi wata, amma nima a duba tawa buƙatan, ina matuƙar ƙaunarki Hajiya Ramla, a taimake ni, idan ban same ki ba akwai mastala babba ma kuwa." Furucin Abbaa na idan bai sameta ba akwai mastala babba, dariya ya bata, dan haka ta maste dariyanta, ta murmusa kawai, a ranta mamaki take irin na halin maza, wato manya da yara duk daɗin baki ta cika su, namiji ya dage da idan bai sameki ba kaza-kaza, amma abu mai wuyan ki amince ne ayi auren, shikkenan kin zama permanent kuma sai haƙuri, idan ba ki yi sa'a ba baƙin cikin yau daban na gobe daban, to dai Allah kyauta ya kuma haɗa kowa da sa'ar sa yayi dacen samun na gari, amma sam-sam halin wasu mazan bai haɗu ba, duk da wasu matan su suke nemawa kan su irin wannan rayuwan, Allah kyauta kawai. Mami murmushi tayi ta ce, "Alhaji ka yi haƙuri, amma dai ni abinda ya dame ni yanzu shi ne ka dawo da Maman Kabeer." Abbaa kallon Mami yayi cikin ido ya ce, "kin tabbata idan ta dawo za ki amince mini ki aure ni?" Murmusawa Mami tayi ta ce, "ban yi alƙawari ba, sai dai shi Danish zai iya zuwa wajan ita Faɗima, idan sun dai-daita taga shi ya fi mata, to shikkenan Allah sanya alkairi, dan abin da yaro ke so shi za mu masa." Abbaa sosai wannan amsa dangane da Danish ya masa daɗi, dan haka ya sa a rai shi ma zai ci-gaba da zuwa yin magiya, har Allah ya sa ta amince dan abin zai fi ba da armashi. Bayan sun gama hiransu, sallama suka yi, Abbaa ya tashi yayi tafiyansa, Mami dai duniyan tunani ta faɗa, juya abubuwa da dama take a ranta, ƙiran wayan da ya shigo mata ne ya kaste mata tunanin, ganin mai kira sai ta saki murmushi ta ɗauka, cikin zazzaƙar muryanta ta ce, "Alhaji bar ka da war haka." Alhaji Mukhtar a ɗaya ɓangaren shi ma yana murmushinsa ya ce, "Barka dai masoyiya ta, fatan kina lafiya، ya kuma yarinyata Banafsha take?" "Duk muna nan lafiya yallaɓoi, ya ƙasar mutane?" Faɗin Mami. Alhaji cewa yayi, "Lafiya Alhamdulillahi! Ga mu cikin ta, sai fama nake da kewanki, yanzu badan-badan ba ai da kuɗin jirgi zan miki ki biyo ni, ko kuma ma na sakoki a gaba mu taho tare, ga shi duk mutanen ƙasar masu irin kyawunki ne." Mami cikin ƴar shagwaɓanta ta ce, "To ai ni na ɗauka ma ka dawo, sai naga ba layin Nigeria ba ne, nima kewanka nake, kwana biyu babu customers, ina ga kore su ka yi da za ka tafi, ga shi dai ni a buƙace nake, badan-badan ba nima da na biyoka." Alhaji a nasa ɓangaren dariya yayi, dan yasan watarana Ramla na irin magannan ne da gan-gan dan ya ji haushi, amma abun da bata sani ba shi ne, wani irin soyayya yake mata wan da ko turmi da taɓarya ya kalleta da namiji, to ba zai cire masa son ta ba, shi baisan ko dan a cikin irin rayuwan ya san ta bane, amma shi a haka ma yake mugun ƙaunarta, yana kishinta ba kaɗan ba, amma a yanzu burinsa ya mallaketa sai yayi kishin yan da ya kamata, sai da ya gama dariya sannan ya ce, "Ko taurarin sun fara yin ƙasa ne mu godewa Allah, amma dai kar ki damu soon za ki ganni, suprise kawai, ki shirya ganina a ko wanni lokaci daga yanzu, tun da kina buƙatata ai zuwa ya zama dole, nima a buƙacen nake, wata biyu ba mata, ina dawowa na bai wa Hajiyata rabonta, zan wuco na zo ke ma na baki naki rabon masoyiya, duk ƙishin sai na kawar miki, ke dai ki adana mini kan ki kar na zo kuma kin riga da kin kashe ishinki ni ki kasa kashe mini nawa." Mami murmushi tayi suka ci-gaba da wayansu cikin soyayya, ka ɗauka mata da miji ne, tuni ma ta mance da wata maganan da suka yi da Abbaa, sai da suka yi sallama sannan ta ajiye wayan tare da yin murmushi, wato Alhaji Mukhtar mutum ne, tun ranan da ta yi kuka ya ce ba zai kuma mata maganan aure ba, to bai kuma ba, sai kawai Mami ta ji ya bata tausayi. Ɓangaren Alhaji Mukhtar da ya kwashe fin wata biyu a Egypt, suna gama waya da masoyiyarsa ya murmusa tare da addu'an Allah shirya su ya dawo masa da ita hanya. Abbaa ko da ya koma ya ƙira Danish akan zai iya zuwa wajan Banafsha, idan ta aminta da soyayyansa shikkenan sai ayi maganan aure, amma ya faɗa masa bayan shi akwai wani mai nemanta. Danish duk da ya kwana da sanin Banafsha na da saurayi, amma ya ƙudurcewa ransa sai ya ka da saurayin nata, shi yanzu ko bin mazan da ya ce tana yi baya gani, wani mugun son ta da ƙaunarta ne yake damunsa, burinsa kawai ya mallaketa, dan haka tsaff ya shirya wannan satin ya taho Mubi. Ɓangaren su Banafsha sun duƙufa akan karatunu musabaƙan da za su yi, gaba ɗaya yanzu ko Malam Abbo sai ya dage yake samun lokacinta, ga shi tsakaninta da Maminta indai ta mata maganan aure to ranan sai Mami ta saka ta kuka, ita ta dage sai Mami ta yi aure ita ma, ko kuwa ta koma wa danginta, sannan za ta yi aure, Mami kuma bata amince da ko ɗaya ba, ta dai dage sai Banafsha ɗin ta yi aure. Mami bata faɗa wa Banafsha zuwan Abbaa ba, sannan bata mata maganan Danish ba, ta bar ta dai, idan ya mata ta ji tana son sa, to da kanta za ta yi maganan wanda take so tsakanin shi da Malam Aliyu. Umma tana can zaune a prison har yanzu ba'a fara case nata ba, ko da Mami ta je station ɗin ma akan ta yafe mata a ƙyaleta, amma nunawa suka yi ai case ya riga da ya koma court, kuma ba daman janye ƙara, kuma yanzu a ƙarƙashin ma'aikatan prison take ba ma'aikatan station ba, dole haka Mami ta dawo ba dan ta so ba, yaya babba ko da yaji labari jinjinawa haƙuri irin na Mami yayi, Umaima ma sai ji tayi ta ƙara ƙaunar Mami, Ya Mus'ab ma har da godiya ya yiwa Mami dan sun san yanzu abin zai zo da sauƙi, tun da ta ce ta yafe, ko a court ne to abin da sauƙi. Banafsha da ta ji wai Mami ta yafe wa Umma, sai ta samu Mami ta ce, "Mamina me yasa ba za ki bari a hukuntata ba? Yunƙurin kashe ki fa ta yi, kisa fa Mami, da yanzu na zama marainiya ban da kowa." Murmushi Mami ta yi ta ce, "Innallaha ma'assabirin! Allah na tare da mai haƙuri Banafsha, yafe mata da nayi, sai kiga nima Allah ya dubi wasu laifukana ya yafe mini, ya kuma shirya ni ya dai-daita lamurana, Banafsha ita komai a duniya ƴar haƙuri ce idan ɗan Adam ya gane." Kallon Mamina nayi na ce, "haƙuri Mami? Shikkenan ta yi a banza? Ni fa duk da Umman Umaimata ce amma ya kamata a hukuntata, dan wasu masu irin wannan yunƙurin su hankalta, tun da an ce gani ga wane ya isa wane storon Allah." Murmushi Mami ta kuma yi ta ce, "Ba na yafe mata saboda wasu su ji daɗin aikatawa bane, a'a na yafe mata ne saboda waɗanda aka wa laifi irin nawa ko fin nawa, su ji daɗin yin yafiya da nufin su ma Allah ya yafe musu wani yanki na zunubansu, Banafsha akwai wani kissa daga Manzon Allah SAW kan cewa, watarana a gaban Allah ranan tashin ƙiyama, akwai wani mutum da za'a tattara ladansa a biya bashuka, zalunci, munafurci, ha'inci da sauran su, duk za'a biya haƙƙonƙin jama'a da ya ci, da ladan ayyukansa na alkairi, sai ya zamana dai-dai da ƙwayan zarra ba shi da lada ko guda, to ana cikin haka kuma wani mutumin zai ƙara ɓullowa ya faɗawa Allah, ai shi ma yana bin wannan mutumin bashi dan haka asaka shi ya biya sa, idan Allah ya ce wa wannan mutumi mai laifukan ya ji abinda wannan ya faɗa, sai ya kama murmushi, ko da Allah ya tambayi dalilin murmushin nasa, sai ya ce ai gani yayi bai da lada ko ƙwayan zarra, duk ladan an biya jama'a da shi, yanzu ba shi da komai sai zunubi, Allah ya kuma duban mai kawo ƙara ya ce kai ma ka ji abinda ya faɗa ai ba shi da lada, sai mai kawo ƙara ya ce, in mutumi mai laifin bai da lada, to ai shi yana da zunubi, dan haka a ɗiba, zunubinsa gwargwadon haƙƙinsa da ke kan mutumi mai laifin, a ƙara masa akan nasa zunuban, Allah zai ƙara kallon mutumi mai laifin ya faɗa masa ya ji abinda mai ƙaransa ya faɗa, sai mutumin yayi murmushi ya ce ya ji ya amince, sai Allah ya sa a nuna wa mai laifin yan da jahannama ta ke, idan ya kalli jahannama sai hankalinsa ya tashi, daga dariya ya koma kuka, idan Allah ya tambayesa yana dariya kuma mai yasa ya koma kuka tun da ya yarda, mutumi mai laifin cikin tsananin kuka da tashin hankali zai faɗawa Allah yana son yayi magana da wannan mai ƙaran nasa, to Allah zai basu wata farfajiya su magantu, wannan mai laifin yana kuka zai haɗa mai ƙaransa Allah da Annabi ya taimaka ya yafe masa, idan ya ce a ƙara masa zunubinsa zai ƙara masa azaba ne, kuma idan yana da zunubai da yawa to shi ma ba zai hanasa shiga wutan ba, dan haka sai wannan mai ƙaran ya yafe masa, su koma gaban Allah mutumi mai ƙaran ya faɗawa Allah ya yafe ma mutumi mai laifin, idan Allah ya tambayi dalili sai ya faɗa masa ai shi ma yana da zunubi, dan ya ce a ƙarawa wani zunubinsa ba zai hanasa shiga wuta ba, kawai ya yafe, sai yayi haƙuri, to saboda wannan yafiyan da ya yiwa mutumi mai laifin ya kuma haƙura, sai Allah ya yafe musu duka ya saka su a aljanna, saboda Allah ya ce yana ƙaunar masu haƙuri, to sai Sahabbai suke mamakin yan da ake wannan al'amari duka a gaban Allah, Manzon Allah SAW ya faɗa musu abinda ake nufi da wannan al'amari shi ne haƙuri, Allah na tare da mai haƙuri, Allah na son mai haƙuri, Allah yana sakawa ga mai haƙuri, saboda Allah shi ne ahkamul hakeemin, shi ya fi kowa iya hukunci..." Tun da Mamina ta fara wannan bayani na stura mata idanuwana ko kiftawa bana yi, har sai da ta kai aya, sannan na sauƙe ajiyan zuciya tare da lumshe ido na ce, "To Allah ba da lada Mamina, Allah kuma ya yafemu baki ɗaya, Mami amma dan Allah me yasa kika kasa haƙuri da danginki? In kuma ke ce kika musu laifi me ya sa ba za ki je, ki basu haƙuri ba tare da nusar da su fa'idan haƙuri da yafiya ya za su miki, Mami shi kuma mahaifina me ya miki? Ina yake? Mamina dan Allah dan darajan Annabi SAW ki taimaka ki amsa mini waɗannan tambayoyin." Mami murmushi tayi tare da ƙarisa wa da salati Manzon Allah SAW, ta ce, "Insha Allah Banafsha zan ba ki duk amsoshin tambayoyinki amma ba yanzu ba, kuma ba yau ba, ban faɗa rana na amma na kusa sanar da ke komai kin ji, ki yi haƙuri ki ƙara haƙuri." Kwantawa nayi a jikin Mamina ban kuma cewa komai ba, wannan mutumin da muka haɗu da shi a asibiti ne ya faɗo mini a rai, tura baki nayi lokaci guda kuma na murmusa, tuno abinda ya faru, Mamina kallona ta ce, "Lafiya da murmushi haka gudalliyan Maminta." Murmushi nayi ba ɓoyel-ɓoyel na ce, "Mami bansan me ya same ni ba lokacin da kika yi rashin lafiyan nan, amma gaba ɗaya na zama kaman parrot a surutu, wannan Soja da Abbaa ya faɗa miki shi ya biya kuɗin komai, Allah haka kawai na dinga masa masifa na rasa me ya sa, sai kuma yanzu abin nake tunawa, ni da ba halina ba, meyasa na masa haka oho، kuma fa bai biye mini ba, ce mini kawai yayi idiot" na ƙarishe maganan ina tura baki. Shafa kai na Mami tayi tare da sakin murmushi ta ce, "Allah ya amsa albarka ya saka masa da alkairi, ga shi ko sunansa ba mu sani ba, wannan su ne masu yin abu dan Allah, fisabilillahi, ke kuma Allah shirya mini ke, ai daman Banafsha bakya ji, kin cika stiwa da manyance." Tura baki nayi, muka ci-gaba da hiranmu da Mamina tana shafa kai na, gaba-ɗaya hasaso wannan bawan Allah kyakkyawan soja nake ina murmushi, har ban sani ba bacci yayi gaba da ni. Danish kuwa tun da ya zo ya ji labarin abin da ya faru, ba ƙaramin damuwa yayi ba, musamman da ya kasance shi ne sanadin komai, haƙuri ya bai wa yaya babba, bayan ya masa faɗa sosai, tare suka shirya suka tafi wajan Umma, amma da ƙyar aka bar su suka kalleta, nan ma sai da Danish ya bada kuɗi masu yawa na cin hanci. Duk maganan da suke yi Umma ko ƙala bata ce musu ba, bayan amsa gaisuwansu da ta yi, tambayan Umaima tayi da kuma matar yaya babba ko ta haihu, bayan sun bata amsa shiru ta ƙara yi, gaba-ɗaya sai tausayin mahaifiyarsu ya rufe su, ta zama abin tausayi ta rame ta yi baƙi, shiru ta musu har lokacin su ya cika, suka tashi za su tafi, sannan Umma ta buɗe baki ta ce, "idan yayi ku kawo mini Autana Umaima na gan ta." Cikin tausayin Umma, yaya babba ya ce, "Insha Allah Umma za'a kawo miki ita." Ficewa suka yi suka tafi, daga nan kuma suka ci-gaba da tattaunawa akan yan da za su yi Ummansu ta fito. Gaba-ɗaya mun zama busy a maganan makaranta, ko kaɗan duk ƙoƙarin Ya Danish na ganin ya samu daman stayuwa da ni ta ƙi samuwa, har ya cinye weekend nasa, yau Sunday zai koma, dan haka yau ya dage komin dare to kamun ya koma sai ya haɗu da ni. Ni da Umaima mun je tahfiz na yamma, mun dawo, muka yi wa junanmu sallama, ta shige gidansu nima na wuce namu, kai na a ƙasa ina sakin murmushi ni kaɗai, saboda hiran Soja muka gana yanzu da Umaima, ba tare da na kula ba na ji nayi karo da mutum na yi baya zan faɗi, sai aka riƙo hannuna, idanuwana a lumshe nayi hamdala sannan na buɗe su na ɗago ina faɗin, "Na gode....", maganan baki nane ya maƙale ganin wanda na yi karo da shi, kuma ya riƙe ni ban faɗi ba. Haɗe fiska nayi na ce, "Allah ya isa na, hannuna da ka taɓa." Maimakon na ga ya ɓata rai, ya fara ci mini mutunci yan da ya saba, sai naga saɓanin haka, murmushi yake sakar mini tare da faɗin, "Afuwan gimbiyata." Ƙara kallonsa nayi dan na tabbatar da shi ya faɗi abin da kunnena ya jiye mini, murmushi ya sakar mini tare da ɗaga gira guda. "Hmmn!" Na faɗa tare da jan dogon staki, fiskana a haɗe na ce, "let me have my way." Murmushi yayi ya ce, "faɗa da hausa gimbiya." Wani bansan harara na aika masa da shi, sannan na ce idan ya na yiwa Allah da Manzonsa ya bar mana ƙofan gidan mu. Ya Danish ko a jikinsa, ya ce, "Nima ya zama gidanmu ai, please Beb ki saurare ni, da farko ku yi haƙuri da abin da Umma ta yi, duk nine na ja, amma dan Allah a yafe mata, ki taya ni bai wa Mami haƙuri, Insha Allah next week zan shiga na bata haƙurin da kai na, and beb please ki yafe mini abubuwan da suka faru, ba da intention nayi ba, sharrin shaiɗan ne da kuma soyayyanki." Maganansa dariya ya bani, amma duk da haka na maste, ko kallonsa na ƙi yi, har Ya Danish ya gama shirmen maganganun sa ya tafi ko ƙala ban ce masa ba, yana barin wajan na ja dogon staki na shige gida, ina faɗin, "Ni za'a renawa wayo ɗan iska mara kirki, in ma da wani salon ka zo to duk ina dai-dai da su." Ya Danish cikin farin cikin ya bulbular da abin da ke ran sa ya tafi bayan ya ce mata, "ILOVE YOU BEB", ko cikin gida bai koma ba, ya ja motansa yayi gaba, shi ko haka ma Alhamdulillahi ya gode wa Allahn da ya jarabce da da soyayyanta. Ni kuwa mita na dinga yi, har Mami ta gaji ta buge mini baki, tana tambayan menene ya faru, faɗa mata nayi, maimakon ta goyi bayana, sai naga tana murmushi kawai, ganin haka ƙara kuluwa na yi, a haka kuma da fushina nayi bacci, Allah ya so ma idan na tuno soja inajin kukan ya tsaya sai kuma dariya akan abin da ya faru ranan. Tun daga ranan duk bayan kwana biyu sai na ga ya Danish a Mubi, kuma idan ya zo ya dinga takura mini kenan, wulaƙancin da ya mini, ba irin wan da ban rama ba, har ma da alakoro na masa, amma ko a jikinsa. Mami ta dage da maganan aurena, yau Alhamis muna zaune, Mamina ta ci kwalliyanta, daman jiya ta yi kistonta har da ƙunshi, ba tare da ta kalleni ba ta ce, "Faɗima." Murmushi nayi na ce, "Naam Mamina." Mami ta ce, "faɗima ki stayar da mutum ɗaya cikin masu nemanki, idan Aliyu ne ki faɗa masa ya turo, idan kuma Danish ne, za mu yi magana da Abbaanku, daman ina tunanin ko shi zai ba da aurenki." Murmushin taƙaici wan da ya fi kuka ciwo na yi, na ce, "Mami ban da uba ne? Ko da gaske ba ta hanyar Sunna kika same ni ba, Mami wallahi idan ba auran mutum kika yi ba, ni ban yarda ya zama waliyina ba, kuma Allah sai ana auren na gudu, nima na shiga duniya kawai kowa ya huta, nima na ɗaura daga inda kika tsaya..." Ban ida rufe baki ba na ji sauƙan mari a bakina, wan da take bakina ya fashe, Mami cikin surutu take cewa, "Banafsha wato dan ina miki shiru, shi ne kika dage ko? To kuwa zan nuna miki ni ce mahaifiyarki ba ke kika haife ni ba." Idanuwana a bushe ba ko alaman hawaye na ɗago su, cikin dakiya na ce, "Mami ko kasheni za ki yi, ba zan auri kowa ba sai kin yi aure, Mami ke fa ranan kika faɗa mini Allah na son mai haƙuri, to me yasa ke ba za ki kasance cikin waɗanda Allah ke so ba? Me yasa ba za ki kasance cikin masu ɗaukan ƙaddaransu ba? Mami me yayi zafi shi ba wuta ba, Mami duk fa tsanani na tare da sauƙi, Ya mahaifiyata ki yi haƙuri, amma a yanzu ki samu Abbaa da maganar nan, kema kin san ba ki yi adalci ba Mami, kin ƙi sa kuma ki ce yayi wa yarinyar ki walittaka, ki duba lamarin da kyau." Mami masifa ta fara mini, in da take shiga ba nan take fita ba, ni kuma yau na dage ba zan yi aure ba sai ta yi, saboda ɓacin ran da Mami ke ciki tuni ta fara jibgana yan da muka saba idan na mata irin magannan, duk dukan da Mami ke mini bakina bai mutu ba, kuma babu ko ɗigon hawaye, abu ɗaya kawai nake faɗi, "wallahi Mami ko kasheni za ki yi, ki kashe ni, na yafe miki kuma, amma ba zan yi aure ba sai kin yi..." Ban fasa surutu ba, Mami bata fasa dukana ba, muna cikin haka sai ganin Alhaji Mukhtar muka yi, ba zato ba tsammani, Alhaji da sauri ya janye Mami ya riƙe hannayenta yana faɗin, "Ramla ba ki da hankali ne? Me ke damunki? Kashe ta za ki yi?" Mami kawai fashewa tayi da kuka ta ce, "gwanda na kashe ta na huta, tun da baƙin ciki da damuwa ita ma take son cusa mini, in kai ta mahaifinta an faɗa mata tana da uba ne? Bayan sanadinta na rabu da kowa nawa, farin ciki na, mai so na, iyayena, dangina,mastayi na, da komai nawa, duk dan saboda ita na haƙura da su, na zaɓe ta akan kowa nawa, har sau nawa take so na dinga sadaukar mata da farin ciki na? Haka iya wan da na mata bai isheta ba?" Jin furcin Mami tuni hawaye yayi shaɓe-shaɓe a fiskana, kuka na kama bilhaƙƙi kaman rai na zai fita, me Mami take nufi da bata san uba na ba? Mutum na fita a jikin bishiya ne? Ko mace na haihuwa ita kaɗai ba tare da namiji ba? Ɗagowa nayi ina kuka na ce, "Mami bayan jin wannan furucin naki, sai na kuma samun ƙwarin guiwan ƙin aure, Mami ba zan yi aure ba sai kin yi, kuma sai kin koma ga danginki.." Kamun na rufe baki Mami ta iyo kai na, ta hau jibgana, da ƙyar kuma Alhaji ya riƙe ta bayan ya ce na tafi, haka na tashi ina haɗa hanya na nufi ɗakina, amma ina shigewa kamun na isa ga gadona, tuni wani mugun jiri ya ɗibeni, inajin jiri-jiri, baya na yi luuu na faɗi, lokaci guda numfashina ya ɗauke. Ɓangaren Mami kuka ta dinga yi sai da Alhaji ya dage da lallashi, cikin soyayya yake lallashinta ya ce, "haba Ramla, da girmanki da tunaninki da komai naki, kike irin wannan furucin? Me yasa ne wai ke baki yarda da ƙaddara ba? Me yasa ba za ki mata abin da take so ba?" Mami kuka ta dinga yi mai matuƙar ciwo da cin zuciya, ba abinda take nanata wa sai istigfari, bayan Alhaji ya gama lallashinta da mata nasiha, sai ya ga kawai ta miƙe stuttt! Kaman wacce aka stikare ta, share hawayenta ta ci-gaba da yi, tana faɗin, "faɗima zan yi abin da kike so in zai sa ki farin ciki ki kuma yar da ki yi aure.." tana magana ta wuce ɗakin Banafsha, sai dai tana shiga daga bakin ƙofa ta tarar da ita a yashe a ƙasa bata ko numfashi. Mami ganin haka, ihu ta stala tare da faɗin, "innalillahi wa inna ilaihirraji'un! Faɗimana kada ki mini haka." Alhaji jin ihunta ya shigo da sauri, ganin halin da Banafsha ke ciki, da sauri ya ɗauke ta yayi waje da ita, Mami haka ta bi sa ba mayafi, sai shi ne ya koma ya ɗauko mata, sannan ya ja mota suka yi asibiti, Mami sai ƙoƙari take wajan danne ƙwallan da ke fito mata, kada ta yi hawaye wa yarinyarta. General hospital Alhaji ya kai su, suna isa kuwa cikin sa'a suka samu Dr Arshan na duty, yana ganin Mami ya ganeta, nan yasa aka yi da Banafsha emergency, sai da ya dubata sannan ya sanar da su Mami kada su ɗaga hankali, suma ne tayi saboda wani abu da ta gani ko ta ji ya sa bugun zuciyanta ƙaruwa, ya firgita ta, amma zuwa ba jimawa za ta iya farfaɗo wa, ko zuwa gobe. Alhaji da Mami ne suke zaune a kan Banafsha, Alhaji sai tausan Mami yake yana bata baki, har dare sannan ta farfaɗo tana sumbatu, Mami cikin hanzari ta rungumeta tana faɗin ta nistu ga ta nan kusa da ita, Alhaji kuma ya ƙira likita, sai da ya mata allura sannan a hankali kuma ta koma bacci yayi gaba da ita, tana sakin ajiyan zuciya. Washegari da ta farka jikin ya zama normal, sai da ta ci abinci ta yi sallolinta, sannan Mami ta fara magana cikin lallashi, cewa tayi, "Faɗima ki kwantar da hankalinki kin ji, Inshà Allahu Maminki za ta yi duk abin da kike so da kuma abin da zai saki farinciki, zan yi aure kaman yan da kike so, sannan zan ba ki labarin dangina, zuwa gaba kuma Insha Allah zan haɗa ki da su." Ina daga kwance amma a take na tashi na zauna, kallon Mamina nake cikin farin ciki da ƙaunarta, me nake nema a duniya ina da Mamina? Tuni ma na ji ciwon da ke damuna duk sun fece, karo na farko a rayuwa da naji tabbas mastalana sun ƙare, ko ba komai indai Mamina za ta yi aure to shikkenan, alhamdulillahi abin da nake so kenan, ko maganan danginta bai dameni irin maganan ta yi aure ba, ai rungume Mami nayi cikin farin ciki, ina sauƙe ajiyan zuciya, yayinda Mami kuma ke ƙoƙarin mayar da ƙwallan da ke son zubo mata. Dr Arshan ya zo ya duba ni, da mamaki ya tambayi me ya faru haka, har komai da ke damuna ya setu, daga yanayin bugun zuciya na har jinina da ke neman hawa ya wuce misali, murmushi kawai na masa da yake mun ɗan saba kwanaki da Mami ta kwanta. Sai yamma sannan aka sallamemu, Alhaji ya jido mu muka dawo gida, bayan ya siya duk wani magani nawa da ake buƙata, kuma ya bi mun saya fruits da sauran su. Muna dawowa gida da yake juma'a ne yamma ma ta riga da ta yi, sai ga Umaima ta shigo, ɗakina muka wuce da ita bayan ta gaishe da su Mami, muna shiga ta tambayi me ya faru bata ganni ba tun jiya, kawai faɗa mata nayi ban da lafiya ne, mun je asibiti kuma Dr Arshan ma ya ce a gaisheta. Amsawa tayi ta mini Allah ƙara sauƙi, sai da muka taɓa hira sannan na shiga na wasta ruwa, na zo na kwanta, ita kuma Umaima ta yi wa su Mami sallama ta fice. Mami ta biyo ni har ɗaki ta bani magani da abinci, sannan ta mini sai da safe bayan ta ƙara kwantar mini da hankali, kwanciya nayi ba jimawa bacci yayi gaba da ni. A ɓangarena da yake yanzu na samu nistuwa, ba jimawa bacci yayi gaba da ni hankali kwance. Mami kuwa gaba-ɗaya kan ta chaji ya ɗauka, dan haka ba su wani yi dogon hira da Alhaji ba, ta tashi ta shige ɗakinta, wanka ta yi ta shirya staff sannan ta fito, sai da safe ta yiwa Alhaji, kallonta yayi yana murmushi ya ce, "Ramla sai da safe kuma, ba za ki ce nazo mu kwanta ba? Ko kin manta ke kika ce na dawo kina buƙatata?" Mami murmushin yaƙe tayi ta ce, "Ai nasan ko na ce ba zuwa za ka yi ba, dan haka Allah tashe mu lafiya", ta faɗa tare da shigewa ɗakinta. Alhaji murmushin shi ma yayi kawai tare da girgiza kai, ya ce, "Allah shirya mini ke cikin gaggawa ya nusar da ke gaskiya, ina matuƙar ƙaunarki da kuma buƙatanki Ramla, amma zan ci gaba da kiyaye wa har zuwa lokacin da zan mallake ki, sannan ke ma ina addu'an Allah baki ikon jure naki buƙatan, Allah stayar da duk wani mummunan ƙaddaran rayuwanki haka nan." Mami ko da ta shiga ɗaki, neman baccin tayi sama ƙasa ta rasa shi, kwanciya kawai ta yi tare da zubawa saman ɗakin nata ido, lissafi take akan yanzu wa za ta aura? Alhaji tana son sa ba kaɗan ba, amma tana tunanin kar nan gaba zargi ya zo cikin aurensu ko wani abu daban, tun da ita zuciya sai a hankali balle ma da a wannan harkan ya sameta, sannan Abbaa kuma tana gudun a ƙara samun akasi da Umma, ko kuwa Ummu ma ta kasa haƙuri nan gaba da kawo gori da tashin hankali stakaninsu, kishi masifa ce, duk iya daurewanka watarana sai an samu akasi, sannan bata buƙatan auren da za ta yi saki ya biyo baya, Abbaa tun da ya saki Umma uwar ƴaƴansa tana ganin ita ma zai iya sakinta watarana idan ta aure sa, Alhaji kuma idan ya zarge ta zai iya sakinta shi ma, kuma bata fata da addu'an tayi aure ta fita, cikin mugun damuwa Mami ta busar da zazzafan iska a bakinta, a hankali ta buɗe baki ta ce, "Allah ka mini zaɓin alkairi, Allah Astagfirullah! Na tuba maka Ubangiji na." Haka Mami ta kasance cikin zullumi, wan da har kan ta ya fara ciwo saboda tunani da nazari, so take ta yi auren saboda Allah kuma saboda Banafsha ma ta yi, ita ba ta da farin cikin da ya wuce mata tilon ƴar ta, kuma bata da burin da ya wuce ta aurar da ita cikin aminci da mutunci, dan haka za ta iya yin komai dan Banafsha, har da bayar da ran ta ma. Daga ƙarshe Mami yanke hukuncin yin istihara ta yi(neman zaɓin Allah), tashuwa ta yi ta ɗaura alwala ta zo ta tayar da nafilanta raka'a biyu, sai da ta idar sannan ta karanto addu'anta ta gabatar da buƙatanta ga mahaliccinta, sai da ta idar ta shafa sannan ta samu nustuwa ta bi lafiyan gado ta kwanta. Shi addu'an istihara ba wa iya aure ake yi wa ba, domin an karɓo daga jabir ibn Abdallah, cewa mun kasance tare da Manzon Allah SAW yana nusar da mu duk abin da za mu yi, mu nemi zaɓin Allah a kai(istihara), sannan yana koya mana addu'an, kaman yan da yake koya mana Surah daga cikin Alƙur'ani mai girma, kuma ita sallar istihara ba dole sai da dare ake yin ta ba, ana iya yin ta da safiya, da marece, da dare, da rana, hatta bayan la'asar da ba'a mata nafila, to mutum zai iya yin wannan sallah ta istihara, raka'a biyu sallama ɗaya, idan mutum ya idar, zai karanto addu'an kaman haka :- ALLAHUMMAH INNI ASTAKIRUKA BI ILMIKA, WA ASTAƘDIRUKA BI ƘUDRATIKA, WA AS'ALUKA MIN FAD'LIKAL AZIM, FA'INNAKA TAƘDIRU WALA AƘDIRU, WA TA'ALAMU WALA A'ALAMU, WA ANTA ALLAMUL GAIBU, ALLAHUMMAH IN KUNTA TA'ALAMU ANNA HAZAL AMRA ( sai ka faɗi abin da kayi sallahn saboda shi anan ) KAIRUN LEE WA FI DINI, WA MA'ASHI, WA AƘIBATI AMRI, FAKDURHU LEE WA YASSIRHU LEE, SUMMA BARIK LEE FIHI, WA IN KUNTA TA'ALAMU ANNA HAZAL AMRA SHARRUN LEE WA FI DINI WA MA'ASHI, WA AƘIBATI AMRI FASRIFHU ANNI, WASRIFNI ANHU, WAƘDUR LIYAL KAIRA HAISU KANA SUMMA RADDINI BIHI. wannan ita ce addu'an, Ubangiji Allah ya tabbatar mana da alakiran rayuwanmu, Allah ya sa mu dace. Washe-gari da safe sai da na lallaɓa na yi wa Mamina ayyukanta, sannan na shirya na fito muka wuce tahfiz tare da Umaima, ga mamaki na Ya Danish na tsaye a ƙofa yana bi na da kallo har muka wuce, amma ni ko nunawa nasan da halittansa a wajan ban yi ba. Mun je mun yi karatu sannan an yanke tafiyanmu musabaƙa a cikin jimeta nan da sati biyu, akan mu sanar wa iyayenmu, kamun malamai za su zo har gida a sanar wa iyayen duk wan da za'a je da shi. Ana tashinmu muka kamo hanyan gida, tafiya muke muna hira, faɗa wa Umaima nake Dr Arshan fa kaman son ta yake, dariya tayi ta ce, "ai ke dai sam bakya gani da kyau, kina ji mutum ya ce yana da mata kuma ba zai ƙara aure ba, balle a masa maganan adalci, shi ne kike wannan batun." Dariya nayi sabo da na tuna, masifan da nayi ranan akan ya duba ɗan uwan soja, bai Duba Mamina ba, shi ne na ce masa baya da adalci, ba zai iya riƙe mata biyu ba, haka muna hiranmu muka tinkaro gida, tun daga nesa na hangi mutum staye a ƙofan gidanmu, kuma sarai na gane Ya Danish ne, haɗe fiska nayi tare da jan staki na ce, "Mutum ba zuciya sam-sam haka Allah ya yi sa, ka gama ci mini mutunci ka zo kana ƙoƙarin lashe aman da ka yi." Umaima murmushi tayi dan ta san da wa nake yi, kallon ƙofan gidan mu tayi ta ce, "Masoyiya a taimaki yayana, Allah jiya ma in faɗa miki shi ya sanya ni zuwa na dubo ki ko lafiya, da na ce masa ba ki da lafiya kada ki ga yan da hankalinsa ya tashi, har ya bani tausayi, na ce Allah mai iko, kaman ba shi ya gama miko rashin kirki ba, ga shi Allah ya jarabce sa da son ki, dan Allah Masoyiya ki yi haƙuri ki yafe masa ki kula sa." Taɓe baki nayi na ce, "ke baki san waye yayanki ba ne shi yasa, baki san me ya mini ba, ni da ya Danish ko shi kaɗai ya rage namiji a duniya to ba zan aure sa ba, Malam Abbo na zan aura, Insha Allah." Sallama muka yi da Umaima ta shige gidansu, nima na wuce namu, ina isowa ƙofanmu kaman yan da ya saba ya fara mini magiya, tambayan ya jikina yake yi amma na yi banza da shi na shige gida. Bayan na karya na huta sai Alhaji yayi ƙira na, zuwa nayi cikin ladabi na gaishesa, amsawa yayi tare da tambayan ya karatun namu da kuma jikinsa. Murmushi nayi na ce, "Alhamdulillah!" Jinjina kai Alhaji yayi tare da miƙo mini, leda mai ɗan girma ya ce, "Ga kyautan ki da na yi alƙawari, sannan an faɗa mini result naki, yayi kyau sosai a ƙara mai da hankali, yanzu kuma sai ki faɗi abin da kike so ko ƴar gidan Mami, idan bai fi ƙarfi na ba, Inshà Allah zan miki koma menene." Tun da Alhaji ya fara magana, nayi ƙasa da kai na ina wasa da yastuna, na jima da tanadar amsan da zan bawa Alhaji idan ya bani wannan daman, amma kunya nake ji na rasa ta ina zan fara, ajiyan zuciya na sauƙe tare da lumshe ido na cikin ƙarfin hali na ce, "ka yi haƙuri da abin da zan faɗa idan zai ɓata maka rai, amma shi ne iya abinda nake buƙata." Alhaji murmushi yayi cikin yabawa da hankali irin na Banafsha ya ce, "ina sauraranki Banafsha." A hankali na ce, "Alhaji dan Allah dan darajan Annabi da ƙur'ani, ka taimaka ka auri Mamina, dan Allah ku bar irin wannan rayuwan da girmanku, mu yaranku ba ma jin daɗi musamman ma ni, kuma nasan idan su Majeeder ma za su ji haka ba daɗi zai musu ba, dan Allah Alhaji ku mini wannan alfarman, wallahi shi kaɗai ne abin da nake buƙata daga gare ka, har ma da Mamina", ina gama magana kuka ya ƙwace mini, amma na danne sautin kukan dan kada Mamina da ke kitchen ta jiyo muryana. Alhaji aniyan zuciya ya sauƙe tare da kallona, yana murmushi ya ce, "In Allah ya yarda Banafsha zan auri Maminki, ke dai ki taya ni da addu'a da kuma shawo kan ta, Maminki ce sai a hankali amma in Allah ya yarda wannan karon zan dage kin ji, na miki alƙawarin yin abinda bai fi ƙarfina ba, dan haka auren Ramla bai fi ƙarfina in Allah ya hukunta hakan, kema kuma ina son ki daina saka damuwa a ranki, ki kuma cigaba da yiwa mahaifiyarki biyayya." Jinjina kai nayi cikin gamsuwa da maganansa, na gode sosai sannan na shige ɗakina, wanke fiskana nayi, sannan na buɗe ledan da Alhaji ya bani, kwali ne a ciki, na kuma buɗe wa, ganin wani ranstasten kyakkyawan system tuni na stala ihu ba shiri, ihun nawa har ya jawo hankalin Mamina ta shigo da sauri a firgice tana faɗin, "lafiya Banafsha? Menene ya saka ki ihu?" Cikin farin ciki na nuna mata system da ke hannuna, ita ma da mamaki take bi na da kallo ta ce, "Banafshaaa ina kika samo computer?" Ina murmushi na ce, "Alhaji ne ya bani yanzu, wai shi ne kyauta na", ina faɗa na rungume Mami cikin farin ciki, ina faɗin ta tayani gode masa. Abubuwan cikin ledan na ƙarisa cirowa, nan kuma wani sarƙa ya faɗo da ɗan kunnensa da zobensa, da abun hannu, masu shegen kyau da ɗaukan ido, Mami da ke staye, waro idanuwa tayi ta ce, "Gold dai?" Ai ban staya ba, na fice palourn, amma na samu Alhaji baya palourn yana cikin ɗakinsa, komawa nayi ɗaki cikin farin ciki, ina kallon kyautan da Alhaji ya mini, sarƙan gold, system, ga kuma wani haɗaɗɗen dogon riga wan da kana gani kasan ya ci uban kuɗi shi ma, kayan ma dai ka san ba na Nigeria ba ne, farinciki kaman nayi yaya. Mami komawa tayi ta ƙarishe aikinta, ta shirya sannan ta shiga ɗakin Alhaji, samunsa tayi yana waya da yaronsa, murmushi tayi tare da zama a ɗan nesa da shi, har sai da ya gama, ya dubeta yana murmushi ya nuna mata gefensa, amma Mami sai ta gyaɗa kai kawai, cewa ta yi, "Alhaji sannu da hidima mun gode Allah saka da alheri." Murmushi Alhaji yayi ya ce, "Kada ki gode mini Ramla, dan kin cancanci fiye da haka a wajena, kuma duk wani wan da ya shafe ki zan masa fiye da haka, Ramla soyayya nake miki na tsakani da Allah, ranan na iso ana cikin yanayi mara daɗi ne shiyasa, amma ke ma ga naki staraban na Egypt ɗin", Alhaji ya faɗa tare da miƙa wa Mami wani jibgegen leda. Amsa Mami tayi, tana jin kaman ta rungume Alhaji, amma tasan ba zai so haka ba dan yan da yake gudun abinda zai saɓawa Allah, ita kuma ba za ta masa abin da bai so ba, dan haka cewa tayi, "To ka zo mu karya rankashidaɗe." Alhaji miƙewa yayi da murmushi ya bi bayan Mami, ni ma Mami ƙirana ta yi, duk muka karya, na godewa Alhaji sosai, amma ya nuna ba komai nima ƴar sa ce. Mami kuwa kayan a Alhaji ya kawo mata, dogayen riguna ne na Egypt masu shegen kyau kusan kala biyar, sannan da wani haɗaɗɗen waya ta yayi Redmi, ga turaruka, ita ma har da sarƙanta na diamond, da takalma, sai kuma wasiƙan soyayya da ya jefa a ciki, Mami duk da ba wannan bane karo na farko da Alhaji ke mata kyauta, amma farinciki kaman ta yi kuka, musamman kalaman da yayi amfani da su a wasiƙan nasa. Washe-gari Lahadi, muna zaune da Alhaji da Mami sai aka mana sallama, Alhaji ne ya fita ganin mai sallaman, gaisawa suka yi, da ya faɗa masa ya zo gaishe da Mami ne sai ya masa iso, tun da ya shigo nake kallonsa da mamaki, Ya Danish a cikin gidanmu, yau wace rana, amma sai na dake na miƙe na shige ɗakina ban ce masa ko sannu ba. Mami cikin fara'a suka gaisa da Ya Danish, ya tambayi jikin Banafsha ta amsa masa da sauƙi, suka gaisa da Alhaji kuma, sannan ya ajiye ledan da ya kawo da kaya niƙi-niƙi na dubiya, sallama ya yiwa Mami ya tashi zai tafi, sai Mami ta ce, "Banafshan tana zuwa ko." Ya Danish a waje ya staya jirana, ni kuma ina ɗakina kwance ina danne-danne a system na(🤣su Banafsha duniya sabuwa, ƴan gayu ƴan uwan masu nuƙud), Mami shigowa tayi da sallama, tun da na kalleta na tura baki dan nasan ba zai wuce ta ce naje ba, ai kam hakan ne kuwa, fiska a haɗe ta ce, "kin ga mutum kin tashi kin gudo ɗaki, ko gaisuwa babu kuma kin san wajanki ya zo ko, to maza kamun na ɓata miki rai ki tashi ki je waje yana jiranki, kuma idan kika amsa rashin kunya sai na saɓa miki, yarinya hankali sam-sam babu, wa ya faɗa miki ana wulaƙanta ɗan adam, maza tashi ki wuce", Mami na gama magana ta fice tana ƙwafa. Ni kuwa tura baki nayi, sannan na miƙe, mayafi kawai na yafa na fice, fuuu! Haka na wuce su Mami a palour na yi waje, a cikin haraban gidan mu na tarar da shi, ƙara haɗe fiska nayi sannan na ƙarisa wajan da ya ke tsaye, ko kallonsa ban yi ba balle ya sa ran zan masa magana. Ya Danish cikin damuwa ya ce, "dan Allah kiyi haƙuri ki yafe mini, haka nan ki kulani Banafsha, wallahi da gaske nake son ki, kibar tunanin wani abu, idan kuskuren da na aikata rana ne ma wallahi ba da niya na yi ba, kuma ko da ace Abbaa ba su iso sun same mu haka ba wallahi ba zan iya ƙeta wa wata mutunci ba balle kuma ke, ki yi haƙuri." Tsaki na ja na ce, "Dole ka ce ba da niya ba tun da dole aka saka ka, ka yage mini hijabi, ka haɗa jikinka da nawa, har da bakinmu ka haɗe, sannan a haka ka ce ba niya? Ka dai ji baiwa ne a jikin sai ka ga gwanda ka yaudareni ka aure ni ko, to bari kaji ko maza sun ƙare ba abinda zan yi da kai, ballema ina da wanda nake so, kuma kwanannan za ka ji an yi aurenmu." Danish ji yayi kaman ta wasta masa ruwan zafi ne a zuciyarsa da wannan kalaman, kaman zai yi kuka ya ce, "Wallahi sharrin zuciya ne, saboda irin kalaman da kike faɗa mini.." Saurin dakatar da shi nayi na ce, "nake faɗa maka ko kake jifana da su? Ko ka mance ka ce mini ƴar iska mai bin maza? Ko ka mance cewan da ka yi bana da abin da za ka taɓa? A haka ka yi kokarin ƙeta mini mutunci ka kuma zo yanzu da niyan aurena wai a faɗanka, duk ka mance abin da ka faɗa ne? Ta ina naga abinda za ka taɓa? Sannan ka ƙirani da mara tarbiya, shashasha ƴar iska, ka sanya hannunka a jikina kuma da sunan duka, ban da duk waɗannan ma abu mafi muni da na stana a duniya, sunan da bana son sa bana ƙaunarsa, sunan da yake ƙaddara ga rayuwata, ka ƙira ni da shi Danish, ƳAR KARUWA MARA TARBIYA, ka faɗa mini, sannan a haka kake tunanin na so ka har na aureka? To tabbas ka yi wa kanka ƙarya, dan na staneka! Na staneka! Na staneka! Bana ƙaunarka bana son ka, bana son kallonka, ko mai irin sunanka bana ƙauna, kai ka sa na stani maza na stani aure, amma Alhamdulillahi yanzu da nayi gwanina mai ilimi da sanin ya kamata to naji ina son aure kuma zan aure sa." Ya Danish runste ido yayi kaman wan da aka kikkifawa mari, guiwansa ya saka a ƙasa ya ce, "Duk abinda kika faɗa ba sharri na faɗe su kuma na yi su, baki ƙara komai ba sai ma ragewa da kika yi, kuma nasan na yi ba dai-dai ba, ban kyauta ba, bayan haka uwata ta yiwa mahaifiyarki illa, dan Allah da Manzonsa ki yafe mini, dan darajan Annabi ki yafe mini, duk abin da na miki kuma idan ba ki manta ba, babu wanda baki rama ba a take ma kuwa, sannan ga shi Allah ya ɗaura mini soyayyanki, ki yi haƙuri Banafsha, ina sonki ina ƙaunanki dan Allah, ko da baki aure ni yanzu ba, zan zauna dakon jiranki har idan Allah ya sa ke rabona ce, to mijin zai bar mini ke ko kuwa zai mutu na aureki." Jikinane yayi sanyi saboda yan da ya haɗa ni da Allah da Annabi, wan da ya halicce ni da kuma wan da aka halicci dubiya baki ɗaya saboda shi, Allah ya wuce komai ya wuce abin wasa, sannan kana ɗan Adam bai kamata a ce ka yi abu dan Allah ko Annabi ka ƙi yi ba, sannan na tuna maganan Mamina na ranan akan haƙuri, dan haka ajiyan zuciya na sauƙe tare da faɗin, "Na yafe maka duniya da lahira, komai kuma ya wuce, amma dai ka sani ina da wan da nake so, kuma in Allah ya yarda idan ya aure ni mutuwanma tare da shi zan yi", ina gama faɗan haka na juya na shige gida. Ya Danish ajiyan zuciya ya sauƙe jin na yafe masa, sai ya ji wani abu mai nauyi ya sauƙa masa a zuciya, domin kuwa tun ranan da yayi ƙoƙarin ƙeta mata mutunci shikkenan abin yake damunsa, tun da yasan nan gaba shi ma uba zai zama. Ni kuwa ina shiga gida na wuce ɗakina, ko ta kan ledan da Mami ta nuna mini ban bi ba. Alhaji dai ya kasa haƙuri sai da ya yiwa Mami magana Danish, faɗa masa komai ta yi bata ɓoye masa ba, har da akasin da suka samu da mahaifiyar sa, da kuma son ta da Abbaa ke yi, Alhaji ya ji kishi jin wani na son Mami har ga yaronsa ba son Banafsha, sai ya ji ina ma shi da yaronsa ne za su mallaki Mami da ƴar ta, amma dai Alhaji sai ya ɓoye bai nuna ba, addu'a yayi kawai da fatan alkairi. Ya Danish a ranan da yamma-yamma ya koma wajan aikinsa, cike da ɗimbin soyayyan Banafsha, musamman ma da ta ce ta yafe masa. Bayan sallahn isha'i kuma sai ga Malam Abbo, Alhaji da yake ya sheda sa shi kam, gaisawa suka yi, suka gaisa da Mami sannan suka bamu waje, sai da na ɗan shafa kwalli da man baki sannan na fito, cikin fara'a muka gaisa da Malam Abbo, nan ya fara baza hajar soyayyansa yanda ya saba, kalamai masu shiga jini da jijiya, su tsaga ƙashi da ɓargo su kai maka har ƙwaƙwalwanka, gaskiya wan da ya ce ustazai ba su iya soyayya ba sai wa'azi to gaskiya yayi kuskuren fahimta, gaba-ɗaya Malam Abbo idan yana kalamansa tafiya yake da tunanina. Malam Abbo ya jima sannan ya mini sallama ya tafi, ni kuwa na shige ɗakina cikin dimbin tunanin Malam Abbo da soyayyar sa da nake ji yana kama ni. Washe-gari Litinin, Alhaji sai da ya ajiye ni a makaranta sannan ya wuce zai koma gidansa, wannan karon bai jima ba saboda yana da shungulla, ina makaranta Malam Abbo ya zo suka gaisa da Mami ya faɗa mata batun tafiyanmu Yola musabaƙa, Mami ta yarje ba komai bayan ta musu addu'an nasara, da kuma roƙon a kula musu da yara, kada a ci amanan iyayen yara a ɓata musu tarbiyya. Bayan na dawo makaranta, Mami ta faɗa mini, sai lokacin ma na tuna nikam, na faɗa mata ai muma an faɗa mana na sha'afa ne, murmushi kawai Mami ta yi ta ce, "je ki wasta ruwa ki ci abinci, idan kun dawo makaranta zuwa anjima za mu yi magana ko." Amsawa nayi na miƙe n shige ɗakina, ruwa na watsa sannan na ci abinci na yi sallah, shirin tahfiz kuma na yi, sallama na yiwa Mami na fice muka tafi tare da Umaimata. Bayan mun je mun dawo, zuwa dare muna zaune da Mamina ta dubeni ta ce, "Banafsha!" Da murmushi a fiskana na ce, "na'am Mamina." Ajiyan zuciya Mami ta sauƙe ta ce, "Banafsha na sadaukar miki da abubuwa da dama a rayuwata, tun kina ciki har zuwan ki duniya, ban taɓa gajiya ba kuma bana fatan gajiya watarana indai zan sa ki farin ciki, kaza bata taka ɗan ta saboda bata son sa, a'a saboda tarbiyya take haka, nasani kina da tarbiyyan da na baki dai-dai gwargwado, kina jin maganata kuma kina kiyaye ɓacin rai ba, Banafsha ina da dalilin ƙin aure, amma kuma dalilin nawa bai kai naki ba na yan da kike so nayi aure, Allah ya ce ko iyayene idan suna ba dai-dai ba ka faɗa musu gaskiya, dan haka zan yi abin da kike so, nasan ke ma ba ƙin abinda nake so kike yi ba, zan yi aure da yardan Allah, zan kuma baki labarin dangina kaman yan da na faɗa, zuwa gaba kuma zan kai ki gare su, aure dai yanzu zan yi, labari kuma zan baki shi ne a matsayin kyautan bikinki, dan haka idan kin amince kin turo miji to kin shirya jin labarin Maminki." Ajiyan zuciya na sauƙe cikin sanyin jiki na ce, "Mami Allah nima ina son ki kuma zan iya sadaukar da komai saboda ke da farincikinki, ki yi haƙuri ki yafe ni idan na ɓata miki." Murmushi Mami tayi ta ce, "Ya isa haka Banafsha, yanzu dai ke ce ƙawar Maminki, ke ce mahaifiyar Maminki, kuma mahaifin Maminki, ƙanwata, yayata, yarinyata kuma komai na, dan haka sai ki bawa Mami shawara wa ya kamata ta aura tsakanin Abbaanku da Alhaji", Mami ta ƙarishe maganan tana murmushi. Wani farinciki ne ya lulluɓeni, tun ba'a je ko ina ba, na fara ganin sakamakon haƙuri da kuma jarrabawan rayuwa da na shiga, Mamina ke mini wannan magana, lallai uwa-uwace, bai ma kamata mutum ya haɗa soyayyan mahaifiya da na kowa ba a duniya, cikin ƙaunan Mamina na ce, "Mami tsakani da Allah da farko Abbaa nake so ki aura, amma yanzu na fi son ki aure Alhaji." "Saboda me kika so na auri Abbaa kuma kika fasa, Sannan saboda me kika ƙi Alhaji yanzu kuma shi kike so Maminki ta aura." Murmushi nayi na ce, "Mami da farko na ga ƙoƙarin Abbaa ne na stawon shekaru yasan irin rayuwan da kike yi amma yake dakon soyayyanki har zuwa yanzu da ya faɗa miki shiyasa na so ki aure sa dan gani ga Umaima ta, amma kuma da wannan abu faru sai hankalina bai kwanta da hakan ba, Abbaa ya saki Umma kuma saboda ke yana son aurenki, to bana son kema ya miki haka nan gaba, sannan kar Umma ta kashe mini Mamina." Murmushi Mami tayi ta ce, "Sayyada Faɗima, ina jinki shi kuma Alhaji fa." "Uhmñ! Mami haushinsa nake ji saboda yan da yake zuwa gidannan yayi kwanaki, kuma da aurensa da yaransa, yana ta ɗawainiya da mu wataƙila baya yi wa matansa da yaransa, shi ne bana so dan kada ya aureki ya miki haka, amma yanzu na fahimci ba haka bane, da gaske Alhaji yake son ki, dan Allah Mamina ki amince ki aure sa, wallahi ko ba za ki kai ni wajan dangin babana ba to na yarda ya bayar da aurena." Mami jinjina kai ta yi ta ce, "Madalla da yarinya ta mai halin manya, tunanin nesa da kuma nazartan rayuwa, Allah miki albarka Banafsha, naji shawaranki kuma na ɗauka indai hakan zai saka ki farin ciki, amma kuma zan cigaba da neman zaɓin Allah, kema ina son ki dage da addu'a da istihara duka, tsakanin Aliyu da Danish Allah zaɓa miki mafi alkairi, idan dukan su ma ba alkairi bane, to Allah baki nagari wan da ya fi su, saboda duk halin da kuke ciki da Danish na sani, ina kallonki ne kawai da ido, to ki dena ki bari bana so, ba kyau wulaƙanta mutum dan ya ce yana son ka, aya ce guda a ƙur'ani mai girma cikin Suratul baƙara da ya ce, "ASA AN TUKRAHU SHAI'AN WA HUWA KHAIRUN LAKUM, WA ASA AN TUHIBBU SHAI'AM WA HUWA SHARRUN LAKUM" dan haka ina son ki cire stanan kowa a ranki ki yi addu'an alkairi kawai, Allah miki albarka ya tabbatar mana da alkairi." Da, "Ameen" na amsa cikin gamsuwa da maganan Mamina. Haka rayuwa ta din ga tafiya Umma har yanzu tana kulle kuma tukunna ba'a fara shari'anta ba, amma dai an kai Court ɗin, kuma ana ƙoƙarin farawa. Ɓangare na kaman yanda Mami ta mini faɗa to naji, addu'a nake na neman zaɓin Allah, idan Ya Danish ya zo ba hantara ba komai zan kulasa amma dai ba dan ina jin son sa a rai na ba, Malam Abbo ma duka ina kula shi. Ɓangaren Mamina ma ta cigaba da addu'a, kuma zuwa yanzu Alhajin ne take jin ya kwanta mata a rai, dan haka ba ɓata lokaci ta fara shiri tana gyaran jikinta, ni ma tana bani wasu abubuwan. Bayan sati biyu komai sai hamdala, Case ɗin Umma, su ya Mus'ab sun dage yanzu dai nan da sati guda za'a fara sauraran Shari'an. Ni da Umaima kuma mun shirya staf dan washe-gari ne za mu tafi Yola ɗin, Abbaa kuma tun da ya je Mami ta basa haƙuri shikkenan ya haƙura ba dan ya so ba, sai dan ganin Mami da gaske take ba za ta auresa ba. Washe-gari ranan tafiyanmu, a ranan matar yaya babba ta haihu, Umaima an kai ta wajan Umma, ta sha kuka ba kaɗan ba sai da Umma ta rarrasheta ta bi ta da addu'an alkairi a musabaƙan. Mun shirya tare da sauran ɗalibai da malamai, mota ce babban ta jide mu muka nufi Yola, sai da muka kwashe awanni uku zuwa huɗu sannan muka isa cikin ikon Allah lafiya-lafiya, a wani babban makaranta aka mana masauƙi, akwai masu kula da mu da komai, ɓangaren mata daban na maza daban, haka ma na malamai, sannan har da jami'an staro akwai ana kula da shige da fice na kowa. Satinmu guda curr a a Yola aka gama musabaƙa, muka juyo cikin farin ciki sai addu'an sauraran sakamako, daga dawowanmu kuma aka fara shirye-shiryen yaye mu, dan ba zai wuce wata biyu ba nan gaba, wan da ake saka ran kamun a yaye mu idan Allah ya sa mun yi nasara a wannan musabaƙa da muka yi, to sai mu je kuma na ƙasa da ƙasa a garin Abuja. Mamina ta ƙira Alhaji ta sanar da shi ta amince da batun aure, Alhaji saboda farin ciki ya rasa ma me zai ce, ko me zai yi, abu na farko dai da yayi ya bata goron kyautan kujeran Makka na albishir ɗin da ta masa ta amince, sauran abubuwan kuma ya ce sai ya zo, sannan ya tura mata kuɗaɗe masu yawan gaske akan ta fara shirya masa kan ta tun yanzu, irin maganganun da Alhaji ya fara faɗawa Mami yana sakin layi tuni ta ji a karo na farko ta fara jin kunyarsa, dan kaman wan da aka ce masa an basa budurwa kyauta. Mami shiri ta fara ba kama hannun yaro, mu kuma lokacin muka fara test a college, idan ka kalli Mamina za ka ɗauka wata balarabiya ce, sosai take gyara kan ta. ⭐⭐ ACM Bunayd gidan Papi ya wuce, yana danna horn aka buɗe masa ƙofa ya shige, da sallama ɗauke a bakinsa ya shige cikin gidan, samun Hajiya Sa'adatu yayi a hakimce a kan kujera tana kallo. Amsawa tayi tare da sakin murmushi ta ce, "Bunayd iso ka zauna." ACM Bunayd murmushin da yake iya leɓensa yayi, a fili ya ce, "Ai gidan babana ne Mom, ba sai kin ce na zauna ba", ya faɗa tare da zama, ya gaisheta. Hajiya Sa'adatu amsawa tayi dan abinda ya faɗa bai dameta ba, tambayansa tayi jikin abokin nasa, ya amsa mata da sauƙi a taƙaice, wayansa ya fidda yana dannawa, sai can ya ce, "Wai ina yaran nan ne na ji gidan shiru?" Hajiya Sa'adatu hankalinta na kwana TV ta ce, "suna sama ne ina ji, kasan Majeeder ba ji take yi ba, ni duka sun fitineni ma, kai ba da haihuwa da yawa ba, kai bakinka yayi stayi, yaushe za su koma gidansu ne?" Murmushi Bunayd yayi ya ce, "Insha Allah gobe za mu koma gidanmu Maa!" Hajiya Sa'adatu juyowa tayi ta kallesa ta ce, "kaga wannan sunan naka na rena mutane ba son sa nake ba, ni ce maa ɗin? To ranka zai ɓaci, ai ita Huraira baka faɗa mata haka Momsee kake ce mata tun da ita ta haifeka ba ni ba, kuma kai ai nan gidanku ne ba can bane gidanku." Bunayd shafa kiston kansa yayi ya ce, "To ai mastala da aka samu kika ki riƙe ni, ita ta riƙe ni shiyasa amma dai ki yi haƙuri Mom, da ni da su Ramla duk abu guda ne, idan can gidansu ne to nima can ne gidanmu, idan kuma nan ba gidansu bane to nima ba gidanmu bane, dan ni nafi son su a kan Majeeder ma." Hajiya Sa'adatu ƙwafa tayi ta ce, "Zan kuwa shiga ƙafan wando guda da kai." Ɗan murmusawa yayi ya ce, "wannan kam sai da Papi, ni ina wando guda xa ta ishemu da ke Mom." Hajiya Sa'adatu murmusawa tayi jin amsan da ya bata, ta ce, "Allah ya shiryaka." "Ameen", ya faɗa tare da miƙewa ya haura sama, samun su Majeeder yayi suna ta hira suna dariyan shirme akan wai wani ya ce yana son Ramla a wajan bikin Ya Abeed, ganin Bunayd sai duk suka yi shiru, suka yi zuru-zuru da idanuwa, waje ya samu ya zauna ya ce, "Idan duniya da gaskiya ku yi hiran na ji nima na samu na yi dariya?" Duk dariya suka kwashe da shi, sai kuma Bunayd ya gimste fiska, ganin haka duk sai suka sha jinin jikinsu, a daƙile ya ce, "maza ku tashi ku shirya na kai ku yawon da kuka ce, sannan muna dawowa ku shirya gobe za mu wuce", yana gama magana ya fice. Su kuma cikin farin ciki suka miƙe, har da stalle, sharp-sharp har sun shirya, sauƙowa ƙasa suka yi suka same sa, nan ya ja su suka fice, yawo ya kai su ba na wasa ba, zagaye Kano suka yi, aje nan aje can, suka je babban Shopping-mall ya musu siyayya, sai dare suka dawo gida, yana ajiyesu ya ce, "Ku tabbatar kun shirya da wuri." Majeeder ta ce, "yaya har da ni?" Haɗe fiska yayi ya ce, "Bayan kin je kuma wani zuwan kikeson yi, wa zai miki karatun?" Tura bakinta tayi, amma Bunayd ko kallonta bai yi ba ya ja motansa tare da yin ƙwafa yayi tafiyansa. Ɓangaren Abeed kwana yayi ƙafansa yana ciwo, ga shi kuma abun daman a cinya ne, daurewa yake ya kasa, a haka ya kwana a daddafe, Nusaiba hankalinta a tashe kaman za ta yi kuka, duk da ciwon da Abeed ya ji mata amma shi take tausayi, ko ta kanta bata yi. Washe-gari da sassafe Abeed ya ƙira Bunayd wanda ya gama shirin tafiyansa staff, Abeed faɗa masa an samu akasi yayi, Bunayd kuwa cewa yayi tun da shi ya kasa haƙuri shi ya nemawa kansa dan haka ba zai hanasa tafiya ba yana da abin yi a gida, dan haka sai da ya biya ya ɗau su Ramla sannan ya bi gidan Abeed, ya jide su suka yi asibiti. ACM Bunayd sai da ya gama seta komai tare da likitan da zai duba Abeed sannan ya masa sallama ya ja ƙannensa suka tafi, Abeed sai ƙwafa yake, ya gode Allah ma an ce mastalan ba sosai bane, kwana ɗaya kawai zai ji sauƙi, idan yana son kada ƙafan ya dinga damunsa to ya bari sai nan da sati biyu zuwa uku kamun ya cigaba da amarci. Jirginsu Bunayd ya sauƙa a Lagos da wuri, tuni dakaransa suka zo suka jide su a airport da shegun motocinsu masu ɗan banzan gudu, har sun nufi banana island amma sai ya ce musu Victoria Island za su kai su, nan suka yi gidan Affa General. Suna isa ya shige ciki, su Suhaila kuma suka tattara kayakinsu su ma suka yi ciki, lokacin General baya gida sai Momsee kawai, dan haka da kanta ta yi wa yaranta abinci ta kai ma Bunayd har sashinsa, amsa yayi ya na godiya, Momsee kunnensa ta ja ta ce addu'a ake yiwa iyaye, godiya kam wannan dama ɗawainiya ne da ke kan su kula da yaransu, Bunayd sosai yake son Momsee, sai da suka taɓa hira ma sannan ta fice ta bar sa, ya ɗan cika cikinsa ya wasta ruwa, lafiyan gado ya bi ya kwanta, amma ya ciro waya ya ƙira Abeed tukunna, yana ɗauka Abeed ba ko sallama ya ce, "mugun ACM kawai, to ta Allah ba taka ba har na dawo gida kuma zuwa gobe zan warke." Murmushi Bunayd yayi ya ce, "Daman ai komai ta Allah ce, kuma dama haka nake so ka koma gida da wuri ka ɗaura a inda ka staya, ba dai ka ce babu haƙuri ba, to ka ji ai, tana tare da kai ka bari ka warke just week kawai ko cinye ta ka yi, amma just 1 night ka kasa, to stayuwan me zan yi nima ga shi na dawo lafiya." Abeed ƙwafa yayi ya ce, "ɗan banzan likita da yake bai da mata may be shi ne wai na jira 2 week's kamun na ƙara, ai ba hauka nake ba, halan bai san daɗin abin ba ne, ko kuwa matarsa Salam ce." Bunayd na dariya ya ce, "sunan wata wai Salamatu ba, hhh, to kada ka haƙura, ai ka dinga ciwo kenan ba ruwanmu." Abeed ya ce, "Zan dai bar ta sati guda ta warke ita ma, amma kuma daga nan ba ɗaga ƙafa, sai dai ciwon ta dinga tashi kullum ina asibiti, ni da matata ma zan koma Adamawan haka kawai,wannan duniyar hidiman ba za ta wuce ni ba, kai amma gaskiya ACM an sha ka wasa, wai yanzu dai kana nufin baka san daɗin tukunyar zuma ba? Hhh honeypot duniya ne, Allah ƙarawa mata lafiya da ni'ima, ni nayi gaba sai ka zo." Waya suka ci-gaba da yi cikin barkwanci, har suka yi sallama Bunayd ya kwanta baccinsa. Ko da Bunayd ya farka mamakin mafarkin da yayi yake, shi har ya mance da wannan yarinyar, ƙwafa yayi kawai tuna kallon da ta masa bai mata komai ba har ya taho, dan idiot da ya ce mata is not enough. Ɓangaren su Abeed haka ya daure yayi 2 week's a daddafe yana kewan tukunyar zuma, amma a ranan cewa yayi baisan zancen ba, tun da garin Allah ya waye, ya fara bin Nusaiba da wani narkakken malalacin kallo wan da sai da ta ji a jikinta yau akwai yaƙin sojoji kuma, dan haka cikin dabara ta ƙara shirya kan ta da duk abin da ya kamata, ta kurɓa, su dangin fruit, a daddafe Abeed ya sa ta shirya suka je gidansu, ko bari bai yi ba sun wuni ya ce su dawo, tun a hanya ya fara rikita mata lissafi, Nusaiba langwaɓe kai ta yi ta ce, "my captain ka bari kada mu yi hastari." Abeed wani kallon so ya sakar mata, tare da faɗin, "your wish is my command babyloff", tuƙi yayi da mugun gudu, suna isa gida kuma ya ɗagata caɗak yayi ciki da ita, tun daga palourn ya fara bata passionate kisses, Nusaiba cewa tayi a bari sai dare, Abeed ya ce baya fahimtan Yaren da take yi, ɗaga ta yayi suka wuce ɗaki, bai direta ko ina ba sai stakiyan gado, ya bi ta ya haye jikinta. Wani irin soyayya suke gwadawa juna mai matuƙar stayuwa a rai da zuciya, Abeed kaman maye haka yake lashe ta ko ta ina, ba abinda yake marari kaman ya ji mandhood nasa a honeypot, haka sai da ya tabbatar ya gama lalata lissafin nusaiba sannan ya fara neman hanyarsa, dan zuwa lokacin Nusaiba ma ta gama goge masa sauran haddan kansa, bata staya wani duhun kai ba ta solle mijinta soso da sabulu, tun da ya isa inda yake son zuwa, kuwa ba abinda kake ji sai sumbatunsa, Nusaiba dai yau zafin da sauƙin, dan haka ita ma taya da kukan daɗi take yi, wan da ke ƙara zautar da shi, stawon lokaci suka ɗauka suna hidima har suka samu nistuwa a lokaci guda, wanka suka yi tare ya gasa ta, sannan suka zo suka bi lafiyan gado suka kwanta. Abeed na tashuwa bacci jin ƙafansa lafiya lau, sai kuma ya fara neman ƙari, nan Nusaiba ta ba da kai bori ya hau, amarci kawai suke ci ba ƙaƙƙautawa. Bayan wani lokaci Bunayd yanzu ya zama so busy, yau yana ƙasar nan gobe yana wancan, yanzu haka ma yana Turkish ne, gidan da Suhail yake a can ya ke zaune, haɗaɗɗen gida ne na gani na faɗa, zaune yake a palourn tare da Suhail suna game wanda ake yin sa a abu kaman tv, ƙira ne ya shigo wayan ACM Bunayd, ganin layin Papi sai ya murmusa tare da ɗauka, cikin zolayan mahaifin nasa ya ce, "good day Sir." Alhaji murmushi yayi ya ce, "Ina farinciki ba zan biye maka ba, albishir." ACM Bunayd ya ce, "goro Papinmu, yau dai nishaɗi ake ji za'a wa ɗan fari albishir." Papi ya ce, "Sai ka cika alƙawarinka, ka mana kaya na gani na faɗa." ACM baisan san da dariya ya ƙwace masa ba ya ce, "Yanzu Uwata za'a yi wa kishiya shi ne ni zan yi kaya?" Papi ya ce, "har da sadaki kai za ka biya, wa ya ce ka yi alƙawari." Bunayd yana murmushi ya ce, "Allah tabbatar da alkairi, in Allah ya yarda komai normal Papi baka da mastala, ni na zama ɗan Amarya ma atou, dan haka zan gwangwaje Uwata Amarya, Allah nuna mana, yanzu dai Papi har za ka ƙara second wife ban yi aure ba, Gaskiya to ba zan bari General ma ya ƙara ban yi ba duk da ba zamu bari ya yiwa Momsee kishiya ba, ita kam tana ƙoƙari, Mamata Amarya ma watarana dole mu nuna mata hali muna taya uwarmu kishi." Dariya Papi yayi ya ce, "Allah shirya ka ya baka tagari, kuma idan ka yiwa matata hali zan saɓa maka ne." Ɓata fiska Bunayd yayi ya yiwa Papi sallama kawai, dan ya ce Allah basa tagari shi ne ran sa ya ɓaci, Suhail da yake yana jin su dariya yayi ya ce, "easy!easy!easy dai ACM." Murmushi Bunayd yayi kawai, a take ya ƙira General ya faɗa masa, sannan ya haɗa su da Momsee ya faɗa mata zai saka mata kuɗi za'a haɗawa Papi lefe, dariya Momsee ta dinga yi, wato shi Bunayd ba ya kishin uwarsa, shi kuwa da an ce baya kishin Mom sai ya ce, ai ita ta ja, wa ya ce ta kasa renon sa, shi ko ajikinsa ya koma ɗan amarya, sai da suka gama magana da komai sannan suka yi sallama. Ya ƙira Abeed ma ya faɗa masa, shi ma Abeed ɗin dariya ya dinga yi ya ce, "Kai fa ɗan iskan yaro ne wallahi, General ya lalata ka da yawa, wato ma ka zama ɗan Amarya?" Bunayd taɓe baki yayi ya ce, "iyye, yanzu ma Momsee za ta haɗa ma mamana Amarya lefe, kuma sadaki ma mai stadan gaske zan biya, Allah dai ya sa kada ta bani kunya, Allah sa ta kula da Papi sosai, kuma Allah sata haihu da yawa ta ci gado tun da Mom bata son gado." Abeed me zai yi idan ba dariya ba, ya ce, "To saura watarana halinka ya mosta ka mata halin ɗan kishiya, ba ruwan Papi da kai ka biya amsa sadaki, tuni ya ci ƙaniyarka." "A'a rabani da mata halin ɗan kishiya, ai ana tare ni da Amaryan Papi ta koma Uwata, na bar wa Majeeder Mom, idan naga tasan duniya ma tuni na ce ta nema mini mata ko a danginsu ne." Haka suka ci-gaba da hiransu suka dara, sai da suka yi sallama, sannan kuma suka ci-gaba da hira da Suhail suna dariya kaman abokai, kuma ba kaɗan ba Bunayd ya girmi Suhail. *** WANNAN SHI NE LAST PAGE NAMU, KUMA ƘARSHEN BOOK 1 SAI KUMA BAYAN SALLAH DA YARDAN ALLAH, DA FARKO NA CE ZAN CIGABA DA UPDATE AMMA DA YAWANKU SUN SAME NI A PC WASU MA A GROUP SUKA YI MAGANA, AKAN MU BARI SAI BAYAN SALLAH, TO BAKOMAI ALLAH NUNA MANA DA RAI DA LAFIYA ALLAH AMSHI IBADUNMU, ZAN YI MATUKAR KEWANKU. MU SHA RUWA LAFIYA MASU DARAJA HABIBTIES, ALLAH SA IBADUN MU KARƁAƁƁU NE, ALLAH KUMA YA SANYA MU CIKIN ƳANTATTUN BAYI. SAI MUN HAƊU A BOOK 2 RAMADAN KAREEM from Uwar batoorl ✍️ # Hareeyh # 09161720046 # 07015870735 # 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩 # 𝙇𝙞𝙠𝙚 & # 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚