Bismillahi Rahamanir Raheem!!! 🙎 'YAR BAIWAH🙎 Maman Ussee Yau yakasance jumma'ah yayinda kowa ke hada hadar zuwa masallaci garin yayi haske gwanin sha'awa kowa lamarin gabansa kawai yake tafe take tana yan wake wakenta dauke da tulu akanta zataje debo ruwa rafi kasancewar yau kasuwar garin nasu so take taci kwalliya Dan zuwa kasuwa Sameera kenan YAr BAiwa ahankali kawarta indo ta lallabo tabayanta tace Keee, hava indo meye haka nihar kin tsoratani wallahi ohh wadda aka kira da indo tayi 😀 tace kekuma gaki da tsoro kamar kura ko samira tayi murmushi tace to sai kawai naganki kwatam toya akayi kawalliya naje gdnku banga ki ba eah wllhi Inna ce ta aikeni sayen omo kinga sauri ma nakeyi tace karna Dade to sa himma nima kinga danakai wan nan din nakare sai mun hadu kasuwa ko taimata sallama suka wuce. Kai tsaye gidansu ta nufa da sallamarta ta aje tulun washh wallahi umma nagaji ke banason shashanci Dan wan nan diban ruwan ne wai kingaji rafin nisa gareshine daxakice wai kin gaji sa himma kiyi wanka kinga ankusa tasowa daga masallaci, kije kasuwar ki yo mana sayayya ta amsa da to tashiga daki ta kwabe kayanta tafito da daurin kirji tashiga bayi tai wanka ta fito tana Shafa mai da hoda nidai gefe nakoma ina kallon ikon Allah anata cika fiska da kwalli da digo digo ohhh dariyace ta kusa subucemin nadai gimtse INA kallon Samira an takarkare ana Shafa Jan 👄 takare takoma fannin sa kaya wasu kaya atamfa ce ba laifi kam a wurin samira da ita a ganinta yau Zata goge sosai. Sameera yarinya ce yar kimanin shekara goma sha Biyu farace ba Sol ba irin chocolate colour din nan Allah yamata baiwar kyau bakinta Dan karami dashi dauke da siraran labba ga hakora farare Sol kanana Jere gwanin sha'awa tanada idanuwa masu kayatarwa irin na mejin bacci sexy eyes ba laifi kam batada jiki kuma baxa asakata layin maras kiba ba masha Allah da ita son kowa kin Wanda yarasa ga tada shaf brain shiyasa ake kiranta da yar Baiwa duk abinda aka fada mata bata mantawa ga hankali uwa uba hakuri batada kiriniya ga basira sai dai kash abu dayane samera batadashi iyayenta talakawane ga samira nason boko kamar me intaga Dan birni cewa take Dan koyamini turaci Allah yayi sameera mai son abu duk abinda tasa kanta to ta rike kenan kuma da an fada mata so daya ya shiga kanta Umma na fito bani sakon so nake nadawo da wuri so nake naje wurin Dan birni kinsan yau yadawo Ohh kekam da naci kike to Allah Bada Sa'a ungo ki sayo min kayan yaji da sukari kinji tace to innna ta amsa tafito tana tafiyarta a hankali ba abinda ke damunta har takai kasuwa tana sayayarta saiga garbati shida tawagarsa suka tareta ke yar Baiwa sunanda kowa ke kiranta dashi kenan. Tin dazu ina jiranki kin shanyani mekike nufi itadai bata ce komai ba ta sadda kanta kasa tana wasa da yatsunta can sai ga Indo ta isu takallesu ta watsar wai kai wanne irin bawo nekai ana soyayya dolene kunbi kun takurawa yarinya kun hanata sakat duk Inda taje sai kunbita kamar wasu mayu. Ke yarinya ki iya bakinki mtseew indo taja karamin tsaki kukan dai anyi shashashai wllhi ilu na tare da garbati yadaga hannu zai mareta sai iro yace kai Narabaka gidansu basa yafiya wllhi kumuje tunda uwarta tazo indo taja hannun samira suka wuce kekam dai kinji haushi su wadan nan banzayen zaki tsaya suna garaki to indo yakikeso nayi dasu kinsan halin garbati zai iya kullamin sharrin da banjiba bangani to ki tsaya sokonci har a Rena ki in anmiki tsiwa xakiyi kinuna bakya tsoronsu inba haka. Ba kinatare dajin haushi to Inda banxoba fa sai yaya kenan sai ya kuwa illa in rokesu mtseew kinji haushi wllhi yar Baiwa nidai muje kiraka ni nasayowa innata magarya tam muje. Suna tafe suna tadi abinka da kawaye har sun manta Indo kawar sameerace tun suna yara sa'an ni. Juna ne gidansu ba wani nisa dagidansu sameera indo akwai tsiwa ga iyayi batada hkr kuma bata daikar raini shiyasa ake shankunta ko a cikin gari uwa uba tanada yayu masu shiga mata gidansu duk Wanda ka taba ka tsokalowa kanka basa Barin kota kwana. Sallamu alaikum inna nadawo xanje gidansu Dan birni akoya min boko to yar Baiwa saikin dawo kardai ki Dade kinji ta amsa da to ta fito da azama zuwa gidansu kabeer duk da tana shakkun Hajiyarsa Dan ta tsaneta hasalima batason yana zuwa gidan baxata manta ranar da takirata da mayya kekam kullun sai kin likewa Dana to ahir dinki sameera bata kawo komai aranta ba ita burinta kawai akoya mata turanci ta iya zata jure duk wani fada na Hajiya matsawar za'ta samu abinda takeso wan nan kenan. Tana shiga gidan saida gabanta yafadi tadai danne ta Shiva cikin gidan kai tsaye falon Hajiyar ta nufa suna zaune ita da 'ya'yanta husnah da yusrah sai kamal kanin Kabeer da Sallamarta tashiga su yusrah naganinta suka washe baki suna dariya ohh Yar Baiwa sarkin son karatu har an iso kenan cewar kamal Hajiya Kareema najin an ambaci sunanta ta hade rai kamar bata taba dariya ba Samira na shigowa ta gaida Hajiyar INA wuni lafiya atakaice San nan taja tsaki mtseew da dawowar tashi baza'a barsa ya huta ba kuma zaki wani zo kidamesa haba Hajjiya meye laifinta nine nace tazo ai dalibata ya kk ya kwana biyu hpe dai kinzo dashiri danyau akwai sababin darussa ta murmusa tace eah uncle to shigo ki zauna kamin naci abinci sai mu fara Husnah kuma Ku shirya musamman ma ke yusrah naga bakya maida hankalinki sosai sunka turo baki hva yaya week end nefa yakamata mu huta kai bana son shashanci kutashi maxa Hajiya kareema hararar samira kawai take itadai ta tsani yarinyar nan nacewa ne da ita to dolene saita iya turanci itada take ba yar kowa ba tashin kauye ko ubanme iya turancin zai tsinana mata oho yarinya kamar mayya tabi ta ha nata sakat itada danta inyazo week end said a dare da rana yana tare da shegiyar yariyarnan sai Yarbaiwa cewar Hajiya acikin zuciyarta. Itadai sameera ta takure gefe jiran fitowar uncle Kabeer kawai take yazo yafara koya mata abinda zata karu tabar gidan yana kamalawa tafito da book rike a hannunsa yace to daliba muje garden ko ta mike su yusrah ma suka biyota suka biyo bayanta suna isa kowa ya zauna a kujera yafara gabatar musu da lesson yayinda yar Baiwa da yayi tambaya take amsawa itada batamada lesson book amma yusrah sai a hankali gara ma Husnah tana Dan ja haka da haka har suka kare kasancewar ba lokaci dayawa 'Yar Baiwa tai godiya takoma ta ma Hajiya sallama ta wuce zuwa gidansu tana zuwa ta rungume ummanta tana murna take Bata labarin abinda aka koya mata haka rayuwar samera takansance har karshen sati itadai burinta tasamu ilmi Dan ta taimaki mahaifanta!!! 2 be continued Maman ussee 🙎 'YAR BAIWAH🙎2⃣ Maman ussee Rukayya 'ya CE ga malan sa'idu ita kadai Allah ya azutarsu da ita bayan sunsha wahala matuka kamin su sami haihuwa shekarar su 10 da aure ko batan wata ba'a taba yiba a gidansa kwatsam sai ga cikin Rukayya ansamu karkuso kuga murna a wurin malan sa'idu ya dauki burin duniya yasaka akan cikin nan mai dakinsa har mamaki take duk da itama tana burin taga kwanta a duniya Dan baxata manta ba ko haihuwa akayi idan taje barka ba'a. Bata jariri wai batasan zafin haihuwa ba Dan haka.Baxa a bata ba tasha kuka amma dayake mijinta na matukar kaunarta sai ya lallasheta da kalamai masu dadi yana kwantar mata da hankali yana lurar da ita haihuwa ta Allah ce kuma Allah yana sane dasu karta damar da kanta wata rana suma Allah zai basu nasu rabon haka ne kam gashi hkrinsu yabasu yau Allah yabaiwa salamatu ciki haka sukayita renon cikin har Allah ya ingantashi Rayuwa kenan(mai hakuri mawadaci) malan Sa'idu mutumin garin Raba ne asalin su fatakene sukanje fautaci gari gari anan ne Allah yaha dasa da salame sunana da ake kiranta kenan jinisu ya hadu sosai Dan ita yar dagacin garin Damagara ce kuma duk bako a gidansu yake sauka suke basa masauki anan me Allah ya hadasu har aure ya shiga duk da dagaci. Baisoba a cewar sa bayason ya baiwa.bako yar sa Dan su danginsu auren dangisukeyi haka salame ta dage sai sa'idu aka wanke aka kaita garin raba duk da sun raina da arxikin sa'idu haka suka baro yar uwarsu suka koma damagara haka kuma rayuwarsu takansance itada masoyinta gwanin sha'awa malan sa'idu marayane su biyu mahaifinsu ya haifa malan sa'idu shine babba sai mai bi masa atine wadda bayan haihuwar tane mahaifinsu yarasu duk nauyin gida yadawo akan Maman sa'idu duk da lokacin. Bai wani girma ba sosai atine na karama itama haka dai sukaci gaba da rayuwa yau da dadi gobe da ciyo har Allah ya tashi kafadarsu Atine kuma tayi aure ta auri Habu Wanda shi a birni yake zama da akayi aure yadauki matarsa suka koma can da zama sai dai insunxo ziyara Haka rayuwa tasance gwanin sha'awa salame da sirikarta bamai jin Kansu har aka wayi gari ta haifo santaleliyar yarta mai ban sha'awa kowa sai santin 'yar yake kamar kasace ka gudu daranar suna ta zagayo aka saka mata Rukayya sunan mahaifiyar Maman Sa'idu suna kirantada 'yar baiwa kasancewar Allah yamata hkr tun tana karama batada hayaniya ko wanason Rukayya haka ta taso cikin kulawa ga takwararta na sonta bataso taji kukanta ko wasa ake aka doketa yanxu nan zakaga Baaba ta daura ta yafa wai sai taji mafarin dukan yar lelenta abinka da yara kowa shakkar taba Yar Baiwa yake Dan kar yajaxama kanshi mita a wurin Baaba Dan har gidansu mutun takanje idai game da yar Baiwane Luv u all my fans Maman ussee 🙎 'YAR BAIWAH🙎5⃣ Maman Usman Haka suka ci gaba da ratsa sabara har suka cinma titi sukaita tafiya tun Rukayya na kallon gari gari har ta gaji tai Bacci tasake farkawa kuma basu kaiba. Ai kuwa basu suka isa garin sokoto ba sai misalin karfe 6 na yamma suna isa suka dauki hanyar arkila federal lowcost adai dai saitin wani gida ma dai daici yayi faking kamin nan ya umurci Rukayya data fito bayan ta fitone ya bude both ya Ciro mata yar Jakarta ya CE shiga mana ai nan gdnku ne ta dauki jakar ta shiga cikin gdn shi kuma ya bude get yasaka mortar a cikin gida San yabi bayan Rukayya. Da sallamar sa ya shiga cikin gidan yana kwalawa Atine kira maman sajeeda maman sajeeda kin gammu sai yanxu ko oyoyo Abba cewar Abdallah yaxo da gudunsa mahaifin nasa yadaga sa sama yana dariya sweet boy ya ina mamanku da Auntynku suna kitchen cewar fadil daya fito da niyar zuwa masallaci ya gaida Abban nasa yaja hannu Abdallah suka wuce Atine tazo ta rumgumeshi sannu da zuwa my Dear kunsha Hanya ya INA yar tawa banganta ba au ai na zata tashigo tin dazufa nace da ita tashigo Dan zanshigo da mota kila ko bata gane kofar bane oho bari in dubota daga nan na wuce masallaci da an fara kiraye kiraye ko ta amsa da to. Yar Baiwa kuwa tunda tashiga gidan takasa gane hanya kawai sai kalle kalle take ta Shafa nan ta taba can tanata mamakin ikon Allah can dai ta tsaya a wurin flawers tanata mamakin wai yau itace a birni muryar mutane datajine ya fargar da ita sai ta kewayo ta Inda ta biyo daga farko Rukayya INA kika shigane ko baki gane hanyar bane ta sadda kanta kasa shima murmushi yayi ya ja hannun ta ya kaita har cikin gidan kamin ya koma zuwa sallar magrib, Yarta barka da zuwa ya su yaya da Baaba ta amsa suna nan kalau sunce na gaidaku harma da abu akace na kawo muku tau Rukayya bari yanxu kiyi sallah sai kiyi wanka kici abinci kinji ko bara na kira sajeeda taje dake dakinta saita nuna maki komai kinji ki saki jikinki kinji nan ma gidankune munan iyayenkine ki daukini a matsayin ummanki ki dauki Abban Abdallah a matsayin mahaifinki bakida matsalar komai kinji ta ammasa da to, Kallon falon ta farayi Wanda aka kawatashi da kujeru masu kyau sai kayan kallon da dining area sai kuma dayan gefen store da kitchen sai dakin yara dake kusa da store gefe daya kuma room& falor ne sai dakin me gidan dake kusa da na sajeeda cikin kankani lokaci takarewa gidan kallo a ranta fadi take aljannar duniya dankari Ashe akwai ire iren wadan nan Abubuwan more rayuwa haka tab gaskiya maganar hausawane da sukace nazaune baiga gari ba. Murya Sajeeda CE ta dawo da ita a duniyar tunanin da ta Lula yar uwata zomuje kiyi sallah kinji ta amsa da to yayinda tabi bayan sajeeda dauke da Jakarta a ka suna shiga dakin wani sanyine ya doki fuskar Rukayya tare da daddadan kamshin air fresh sajeeda taja hannunata sukashiga bayi ta muna mata komai kamin nan ta fito ta barta me Rukayya zatayi inba sake baki ba ta fara tabe tabe ba abinda yafi Jan hankalinta irin gani. Kanta datakeyi a mirror sai murmushi take can dai sajeeda taji shuru ba labarin fitowar ta gashi ita har ta gama sallah amma Rukayya. Bata fito. Ba ta kwankwasa kofa yadai Ruky naji ki shuru koda matsalane a San nan ne yadawo haiyacinta ta tuna nan wai bayan gidane ta kunna tap tayi alwala San nan tafito tana fitowa sajeeda ta bata sallaya da hijab ita kuma ta fada toilet Dan tahadawa Rukayya ruwan wanka. Bayan ta kamala sallah ne sai ta karewa dakin kallo ba komai bed ne kawai sai drower sai dressing mirror ba laifi kam gidan ya tsaro sosai bayan tayi wanka ta fitone sai ta Shafa mai kawai sajeeda CE tabata. Body spray tashafa Dan sajeeda akwai son kamshi zata girmi Rukayya kadan Ruky cewar sajeeda kidaukeni a matsayin yar uwarki kuma kawarki nasan bamu wani saba ba Dan ko munje can Raba ba wani dadewa mukeba su mummy sun muna bayanin komai bakida wata matsala kiyi sallar isha sai muje muci abinci kinji 😊 murmushi tayi hadi da yin sallah tana idawar itama sajeeda sallar tafara yi bayan takammala ne suka fita tare suka fito zuwa wajen cin abinci anan suka tarar da iyayesu har sun fara cin nasu sai Abdallah ne yace daddy wan nan CE new Sister dinmu ko ai na Santa a Raba take itace Baaba take cewa yar Baiwa ko aikuwa kowa ya fara dariya kai son ka cika surutu dayawa eah sunanta Rukayya daga yau sister Ruky kunjiko fadil yes momi suka amsa Abin yabaiwa yar baiwa sha'awa a ranta tace lallai inbaka mutu ba zakasha kallo haka akaci abinci cike da raha ana kamalawa sai kuma aka fara labarai anan ne kuma Daddy yafara yiwa Rukayya tambayoyi. Ba laifi tasan wasu wasu kuma bata amsawa sai kuma fadil da Abdallah suka CE su bacci sukeji Sajeeda ma taja Ruky sukabar mummy da daddy a falo. Daddy yanisa gaskiya da ace Baaba bata amince ba da an cuci yariya kinga yanda takeda brain kuwa Dear Mummy tayi murmushi Allah dai yabamu ikon rike amana ameen ta amsa nimafa azo asan yanda za'ai dani Dan ah gajiye nake ya kashe mata ido daya ta murmusa da tasan halin Mijin nata, A bagaren su Sajeeda kuwa banda tadi ba abinda akeyi sun Dade suna fira kamin nan su kayi addu'a suka kashe wuta suka kwanta Rukayya kam godiya takeyi ma Allah wai yau itace a. birni dasunan boko. Muje zuwa kuna tare da Zeenat Yusuf maman ussee 🙎 'YAR BAIWA 🙎6⃣ Maman ussee Tun da asuba mommy tashesu daga bacci Dan su yi sallah bayan sun idar ne kuma suka sake koma wa bacci kasancewar week end ne ba makaranta, Basu suka tashiba ba sai kusan 10:am wanka suka farayi kamin nan sajeeda ta ja hannun yar uwartata domin suje cin abinci Dan tasan yanxu kowa ya tashi dayake al,adar gidan ne atare ake cin abin suna fito gaida iyayensu sunka farayi kamin. Nan Abdallah da Fadil suka gaidasu suma mommy CE tace 'yata bawata matsala saiki Rukayya tace ba komai insha Allah daga nan kuma akayi saving din kowa yafara cin abinci amma banda Rukayya dantakasa cin abinci itasam bata saba dashi ba tafi son dumamen tuwo ko koko da kosai ko waina amma INA ita in cin wan nan kwamacalar, Daddy ne ya kula da ita sai yakira sunanta Ruky ya.bakya cin abinci ne ta sadda kanta kasa cikin in INA tace a gida koko nakesha ko dumamen tuwo ai ko mexasuyi inba dariya ba Mummy CE tace ki Dan Dana mana kiji ai da dadi inbaxaki iya shaba to kici doyar mana tadai daure tayi spoont daya na damar miyar typeyocer din ai kuwa saita hau sha Sajeeda dariya kawai take kasa kasa , Bayan sun kammalane daddy yace dasu su shirya aje islamiya yaushi da kansa zai kaisu Dan ya mika Rukayya nan danan kowa yahau shiri kowa tafito cikin uniform din Islamiya Daddy yafito suka fice gabaki daya mommy kawai suka bari agidan, Abakin get yayi fakin yayinda su Sajeeda suka nufin classes dinsu shi kuma ya nufi office din malamin makarantar yaga batar da Rukayya a matsayin daliba akayi mata tambayi ba laifi kan Dan ko a can Raba tana zuwa makarantar allo bayan an kamla aka bashi takarda yasa hannu yabiya kudi sai suka CE yakoma da ita gobe sai ta fara zuwa kuma da uniform suka sake fadamai dokokin makaranta yayi musu godiya ya ja Rukayya suka tafi a mai makon subi hanyar gida sai taga sunbi wata hanyar mexatayi in ba kallo ba ido ya samu abinci dai dai wata yar plaza taga Daddy yayi parking yace ta jirasa batasan meyaje yiba bai jimaba sosai taga yadawo da Iedoji biyu a hannusa ya. bude set din baya daba kowa yasa su a ciki sa,ilin da yadawo yatada mota suka nufi hanyar gida, Mummy suka tarar harta kammala komai na gyaran gida da Inda sukaci abinci sannu da aiki mommy yara ga kaya nasiyowa Rukayya da yadin uniform saiki bada dinki ayimata iri biyu iri. Nasu Sajeeda Dan gobe zata fara zuwa sauran kayan sa wane nixan fita sai nadawo aff ana manta kinsandai makarantar Boko suna jarabawa ne sai nadawo Hutu zan kaita zadai aci gaba da koya musu extra lesson kamin da dawo hutun Dan naga ba wani Hutu mai yawa bane murmushi tayi hadi da yimasa godiya da fatan alkhairi, Rukayya kuma tana zaune ta kurawa TV Ido ko kyabtawa batayi mummy ta dafata tace muje kitayani gyaran daki sai mu Dora girkin rana Dan su sajeeda sai 4:pm zasu dawo ta fice yayinda Rukayya ta rufa mata. Baya tana nuna mata abubuwa da yakamata ta kula dasu wan nan kenan, A cikin yan kwanaki n da tayi a gida. Bata fuskantar komai sai farin ciki ga soyayya da yan uwanta ke nuna mata suna debe mata kewa sosai sun shaku da sajeeda inka gansu gwanin sha,awa komai tare sukeyi Dan ko a Islamiya tare suke komai sajeeda itace take koya wa Rukayya wasu Abubuwan da bata gane ba cikin sa,a kuwa da am fada ta rike shikenan malamansu har mamakin irin Baiwar da Allah yayiwa Rukayya suke gashidai bawani dadewa tayi ba amma inka ganta saika rantse ta shekera a cikin islamiyar gida kuma ga lesson ana musu badama tana kawo wuta sosai Daddy yasan bayada haufin inya kaita skull za,a sakata aji daya da Sajeeda dayake ita jss 2 take, Tun tanajin kunyar saka wando da Riga harta saba Dan kuwa yanxu Rukayya ta goge dama can ita kai waye ne da ita batada matsala in basuda lesson itada Sajeeda suke taya mummy aikace aikacen gida dayake anyi Holiday. Maman ussee😘 Ina Alfahari da Ku my fans 🙎 'YAR BAIWAH 🙎7⃣ Maman Ussee Haka Rayuwarsu taci gaba da kasancewa gwanin sha,awah har holiday ya kusa karewa yau ya kasance Sunday kowa da kowa na falon gidan anata firar duniya gwanin dadi fuskar kowa cike da annashuwa da anuri Abdallah ne yace Daddy gobe Holiday zai kare kuma kasan kamuna alkawarin zaka mana shopping yau ko Fadil ya amsa eah little bro Mummy tace harda ni kenan za'aje shopping din Daddy yace OK to Ku shirya sai muje tare kunji yes Daddy suka mike Dan shiryawa Rukayya an zama yan gida yanxu kowannen su yafito cikin shiri Rukayya da Sajeeda jalabiyace a jikinsu dark blue sukayi rolling abin yayi kyau fadil da Abdallah kuwa Riga da wandone suka sa mummy itama Doguwar rigace ta shadda taji kwado kai familyn fa sun birgeni haka suka fito suka shiga mota Mummy dasu Sajeeda a Baya fadil da Abdallah a gaba asu zarce ko inaba sai a Zabira shopping mall nan kowa yayi ta zabar abinda yakeso Rukayya dai kasa daukar komai tayi Dan ita kunya takeji Sajeeda CE kedaukar komai Biyu inta dauka saita daukar wa Ruky bayan sun karene sukaje wurin bill akayi bill Daddy yabiya suka sake fitowa kowa sai kallon su yake nusamman Ruky da Sajeeda kamar yan biyu ba karya Allah yayi Halitta Dan ko Sajeeda ba bayaba a fagen kyau, Daddy bai zarce dasu ko,ina ba sai Daddy's smart anan sukaje suka ci abinci suka zaga gari sosai kamin nan suka dawo gida. Gab da magrib suka dawo zubewa sukayi a fallo kowa ya gaji Dan yau sunsha yawo sun more sosai gsky bayan su hutane Daddy yaja su Fadil da zuwa masallaci Mummy kuma ta wuce zuwa dakinta yayinda da umurci su Sajeeda dasuje su yi sallah suma kuma su shigar da kayan ciki haka suka kwashi kayan zuwa Inda yakamata su adanasu. Bayan sun idar da Sallar Isha suka fito bayan aka ci gaba da hira can Daddy Yakira sunan Rukayya, Rukayyatu ki shiryafa gobe zaki soma zuwa skull insha Allah saboda haka saiki shirya kinji murmushin jin dadi tayi yayinda da ta CE nagode Daddy Allah yakara girma bakomai ai kidage dai kinji ko to 'ya ' yan Daddy aje ayi bacci saboda a tashi da wuriko kunji yes Daddy af na manta Ga uniform din Ruky can a bed dina Sajeeda jeki kidauko mata gobe sai a shirya da wur wuri kinji tau Daddy bakida wata matsala Rukayya. Nariga nayiwa principal magana interview kawai za a maki su zasu baki komai da komai saboda haka kidage kawai inkiyi kokari za a sakaki class daya da 'yar uwarki Sajeeda tam ta amsa suka fice dakin su kowa yayi addu'a ya kwanta yayinda 'YAR BAIWAH take farin ciki sosai mafarkin ta yakusa yazama gaskiya. Maman Ussee 🙎 'YAR BAIWAH 🙎 8⃣ Maman Ussee Monday morning tun 6 suketa shirye shiryen zuwa skull Sajeeda CE ke nunawa Rukayya yanda zatasa kayan skull din ,kai gsky fa kinyi kyau tawan kinga yanda skull uniform din nan suka karbeki ta kashe mata idon daya Ruky ta kaimata duka ta goce suka fito falor sunata dariya yayinda su Fadil ma su. Shirya tsaf Daddy kawai suke jira bai wani jima ba ya fito sanye da kayan shi dagani shima aiki zaije daya aje yaran, ba bata lokaci Mummy tai musu addu' a suka fice dukkansu suna daga mata hannu, Bayan sun shiga mota Daddy ya tuka zuwa skull din dake dai dai Bafarawa east, garin yacika sosai da mutane kasan cewar yau Monday masu zuwa skull na fita yayinda masu zuwa aiki ke kama ga bansu da zuwa aiki kai tsaye daddy cikin makarantar ya danna motarsa wato KEY SCIENCE ACADEMY, bawani bata lokaci Sajeeda dasu Fadil suka nufi assembly yayinda Daddy ya nufi principal office da Rukayya bayan yagabatar da ita a fadamai rules din makaranta ya amince kamin nan aka bashi takarda yasa hannu yayi godiya sosai ya wuce yayinda PC ta kira senior master domin a iyiwa Ruky inter view da Name dinta aka fara ta amsa Rukayyat Sa'eed bayan nan kuma sai aka cigaba da yimata sauran questions tana amsawa yanda yakamata, mintuna kalelan aka bata class yayinda aka kira, class master dinsu ya rubuta name dinta a Register kuma aka umurce shi daya kaita ya gaba tar da ita wa yan class as a new student kai tsaye , Jss 2 blocks ya nufa da Rukayya kamar dai yanda Daddy ya. Bukata cikin sa,a kuwa ajinsu Sajeeda ne bayan shigarsu, student suka mike tsaye, Good morning sir, morning how r u today, we are All fine sir, OK sit down, Anan yagabatarda ita yayi kiran register kuma ya umurci class rep data bata set shikenan yafita Dan yagama aikinsa, Fitarsa keda wuya Sajeeda ta doka uban tsalle ta rungume Rukayya tana murna sosai, Hi kinga Allah ya amshi addu,a na ko so yanxu muna class daya if u did not understand anything just ask me 😊 murmushi kawai Ruky tayi hadi da samun set bayan nasu Sajeeda yayinda su Muhibba yan sit dinsu Sajeeda suke tambayar ta dama tasantane eah yar uwatace she's my sister daga nan kuma aka cigaba da gaggaisa irin na new students da old kundai gane😜 uncle me English ne ya shigo da yake ba musulmi bane ya gabatar da lesson dinsa ya kuma basu pappers dinsu na fist term bayan ya kare sai mai science yashigo shima yagabartar da nasa lesson din kamin nan aka buga aje break fast Sajeeda da Rukayya tare suka fito zuwa dinning area anan ne Sajeeda ta ringa nunawa Ruky abubuwa da dama wadanda bata saniba da kuma Inda ake komai da komai haka suka kasance har time dinda aka koma class ba laifi Rukayya ta dage sosai sai sun hada Kansu ita da yar uwarta ba abinda basayi tare har lokacin barin skull din yayi suka shiga skull bus Dan dama ita ke mayardasu gida saidai da safe Daddy ya kawosu su Fadil da Abdallah bangarensu daban kasancewar su a primary suke sunada masu bus din duk da skull din dayace amma kuma Nursery daban primary daban ss da jss ne kawai a hade Sajeeda da Ruky suka shiga tare aka yita sauke wadanda ke kusa yayi da aka zo unguwarsu suma suka sauka sunayiwa sauran yan mates dinsu bye bye sai mun hadu gobe inji su Hibba sajeeda ta amsa da to, Bayan su shiga gida suka tar rar dasu Fadil da Abdallah har sun dawo kasancewar su 12:30 ake tayar dasu sukuma sai 1:30 suke tashi Daddy. Baidawoba haka suka cire uniform dinsu suka sake wanka kamin nan suka saka uniform dinsu na Islamiya da time yakusa yi. A RABA FA? Tun bayan tafiyat 'Yar Baiwah Baaba kullun cikin cewa take harda Dan zazzabin ta na kewar jikar tata kullun ta lisafe da ko kwana nawa yar baiwa tayi a birni kullun tunanin ta yanxu a wane hali jikarta take sai dai zuciyarta tana hayamata duk Inda yar baiwa take to addu,ar da take mata yana tare da ita da A kullun baaba sai taiwa Rukayya addu,a kuma batason taji lbrn komai indai ba firar mutuniyar ta bane hakan CE ta kasance ko a wuri mahaifinta sai dai yana da jarumta baya nunawa dankar ya karyawa baaba zuciya haka suka kasance gidan shuru shuru har na tsawon sati biyu tun basu saba ba har yazama jiki suka saba kowa yadan fara sakin jikinsa aka dawo yanda ake da saidai kuma in an tuna ayi kewa sabo kenan. Maman ussee😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎9⃣ Maman Ussee Ruky da Sajeeda zaune a dakinsu sunata fira sai dariya kakeji wow gsky nazata inaje skull din nan zan fuskanci Matsala, ashe ba haka nan bane, kai dadina dake tawajena tsoro gareki, ninasan ba abinda zai faru kawai dai kedince akwai tsoro. Kinga tashi kar muyi latti kinsan halin mutumin naki mai tajwid akwai disgi ni kuma na tsani mutun mai disgi hakafa ranar safa CE kawai bansaba ya hanani shiga ajin Ruky tace OK kinsan dai gobe akwai Hadda ko saboda haka yau. Ba, bacci Dan kar muje bamuyiba kinga gbe akwai skull cox Hutu yakare yanxu da dare zamu rika yin Hadda dinmu, Bayan sun kammala ne suka fito sanye da uni din Islamiyarsu sama sama suka ci abinci Dan karsuyi latti ayi musu duka sauri sukeyi Rukayya rike da hannun Fadil yayin da Sajeeda take rike da hannun Abdallah Dan a kafa suke zuwa Islamiya tun bayan ranarda Daddy yakaisu, Sunci sa,a suna shiga ana tare yan latti kai tsaye ajinsu suka nufa. Bayan sun aje su Abdallah a nasu ajin. Ai kuwa basu tsiraba Dan koda suka je mai tajwid yariga yashiga hkr suka fara basa dakyar suka ci sa,a yabarsu suka shiga bayan shanyasun da yayi a waje haka yakaraci darasin sa yabar ajin. Basu suka tashi ba sai misalin 6:pm aka tayar dasu kowace daliba ta kama hanyar zuwa gidansu, Ruky da Sajeeda tare da yan kannesu suma suna dai daga cikin masu zuwa gida kasancewar magrib ta kusa da isarsu gida kowane ya nufi dakinsa Dan bayarda farali suna idar da Sallah falo suka xo , a nan suka tararda mummy itama ta fito yaran Daddy sannuku har kunyi sallar ne eah OK to Allah ya karba ya bada lada suka amsa a tare ameen mummy, yadai Ruky hope ba matsala a skull ko karki damu da sannu zaki sabane fatana kawai Allah yataimaka yabada sa,a kuma a dage kunji eah suka sake amsawa, haka sukata fira jefi jefi kiran sallar Isha ne ya tayardasu bayan sun kammalane suka fito domin cin abincin dare, Anan suka tarar da Daddynsu Dan rabon da suganshi tun safe daya ajesu a skull gaida shi suka fara kamin nan kowa ya zauna a set dinsa mummy tayi serve din kowa akaci akasha aka koshi sai kowaya kama gabansa yayinda Ruky da sajeeda suka fara tilawar Haddan su dakuma assignment dinsu bayan su kammala sukayi addu,a suka kwana sai. bacci. Kashe gari haka ta kasance tun wuri suka kimtsa suka fito inka gansu kanar wasu twins gwanin sha,awa yau ma Daddy ne yakaisu skull daga nan ya wuce GT Bank da acan yake aiki bayan an kare Assembly kai tsaye kowace daliba ajinsu ta nufa Dan daukar darasi Sajeeda da Ruky a tare suke tafiya har class dinsu kowace ta zauna a set din ta kamin class master yaxo yakira register daga nan kuma Malami mai lesson ya shigo ya fara gabatar musu da lesson. Maman Ussee😘 Naga sakonku nagode sosai da kulawa nasoyana Allah yabar zumunci. 🙎 YA RBiAWAH 🙎 1⃣0⃣ Maman Ussee Time din break yayi Sajeeda da Ruky suka fito waje class sunayin break yayinda sauran student ke lamarin gabansa, Ruky nikuwa Sajeeda kinsan abinda yake bani mamaki a,a saikin fada wan nan malamin nan na daxu mai disga mutane din nan kinga yanda yabar ummy nata zuba surutu ya kyaleta amma na tabbatar da wani member din class ne daya sha zagi yau kuma na ga sai wani shige mata yake kodan yaga tafi kowa girmane a class din, hey are u jealous 😀 Ruky takai mata duka wane irin jealous kuma ni ina ruwana dashi kawai dai naga hakan baidaceba ne shiyasa na gaya miki OK to kawo takalminki na ajiye miki kije ki gaya musu ustaziya Rukayyatu 'YAR baiwa 😏 dalla Banason rainin hankali daga kawai na fada miki Abu shikenan sai ki wani canja min magana 😀😀😀 dariya sajeeda tayi hardasu kyalkyatawa kamar zata fado kasa aiko Ruky ta ji haushi ta kwashi kayanta fuu ta fice daga wurin hava ke kuwa sorry mana tsayani muje tare INA ko saurarenta bataiba ta fice class abinta sai daga baya ta saiko suka shirya kamin adawo break. Sannu sannu.bata hana zuwa sai dai a Dade ba,a kai ba yau su Ruky zasu zana end of second term examination, a cikin skull kuwa bawanda baisan Sajeeda Abubakar &Rukayya Sa,eed ba komai nasu atare sukeyi duk Inda kagansu tarene ba abinda yake rabasu ko a gida ma hakan ne gasu da ilmi uwa uba kyau gasudai ba wani girmane dasu ba Dan daka gansu zaka yarinta karara a tare dasu sai dai sunada ladabi ga girmama na gaba dasu a class inkaji suna surutu to lallai Abu mai mahimmanci suke tattaunawa. Baruwansu da wasu frnds sudai barsu da karatu Dan kullun abinda Daddynsu yake jaddada musu kenan kosunyi fada to yanxun nan zakaga sun shirya al,amarinsu yana mutukar.birge jama,a ko unguwarsu bamai cewa sun tsokaneshi Dan su karatun ne kawai yasha musu kai alhmdllh cikin sa,a suka fara Rubuta exams dinsu har suka karashe akayi holiday, Murna gurin Rukayya ba,a magana Dan dama ta matsu ayi Hutu Dan taje Raba dama Daddy yace da anyi Hutu zasuje tare suyi one week sai sudawo sabida islamiyarsu dayake sunyi nisa sosai, bayan sun dawo gida da kwana biyar suka daga sai Raba gabaki dayansu harsu Fadil da Abdallah ai kuwa kuxo kuga murna wurin Baaba kamarme taga yan jikokinta musamman ma Yar baiwa taga yanda tayi Haske ta goge hardasu kiba gwanin sha,awa kai lale marhabin da yan sokoto cewar Malan sa,idu nan nan kawai yake da 'ya'yan nasa yanajin wani farin ciki a ransa yarsa CE ta dawo haka tubarkallah masha Allah, bayan an nutsa kowa yaci ya koshi aka fara sabuwar fira yayinda suka gode sosai da namijin kokarin da Daddy yayi musu godiya suka ka rayi da fatan alkhairi, satinsu daya a Raba suka juyo yar baiwa kawai suka bari koshima badan sunsoba saidan rokon da Baaba tayine shi,isa suka barota ta kara sati sai Daddy yazo ya dauketa sukoma, bayan kwana biyu Baaba na zaune itada Rukayya suna tadi take tambayarta bawata matsala daiko eah bakomai lfy lau wllhi bakiga yanda ake bani kulawa ba sosai da sosai to madalla ai hakan akeso Allah dai yasaka musu da alkhairi Rukayya ta amsa da ameen amin shiyasa nake sonki Baabata dankin iya addu,a 😀 dariya Baaba tayi tace ja,ira har yanxu dai sakarcin naki nanan Ruky tace to in ban maki ba wanikeda shi Wanda yafiki ai kekadaice dagake. Bakari 🙊 tabdi wai yar baiwah yaushene kika iya surutu haka lallai zaman birni ya saka ki iya magana 😳ai baaba Dan baki zauna da Sajeeda bane haka take kamar parrot indai surutune uhum menene fara kuma me Ruky zatayi in banda dariya aikuwa Baaba takaimata duka ta goce tsaya kiji parrot akecewa inaga sai naje sake skull dinmu kin kara wayewa ja,ira kekam dai Allah ya shiryeki ta CE ameen tana murmushi. Maman Ussee😘 🙎YAR BAIWAH 🙎1⃣1⃣ Maman Ussee😘 Satin Rukayya biyu daddy yazo yadauketa suka koma sokoto cike da kewar iyayenta musamman ma Baaba dasuka shaku sosai, Haka Rayuwa taci gaba da kasancewa yau farin ciki gobe akasin haka dama ita rayuwa haka ta gada , amma a wurin Rukayya abin ba,a cewa komai Dan kullun cikin farin ciki take yayinda duk tayi sallah saita Roki Allah yasa kama daddy da aljannah hakama mummy dakuma iyayenta. Haka suka karaci holiday dinsu har ya kare duk Wanda yasan Rukayya ada idan yaganta a yanxu bazai ganetaba inhar ba farin sani yayi mata ba Hutu kwanciyar hankali haiba kwarjini duk sun baibayeta batada wala matsala a skull ma hakan ne Dan so dayawa tasha samun kyaututuka da dama awajen malamai kai harma da students akan baiwar da Allah yayi mata ilmi. Ba,a magana Dan ko quiz za,ayi to Ruky da sajeeda na ciki haka ma divert ko inter schools compotions za,ayi to dolene asaka yar baiwa ga tada da speach mai dadinji dakuma saurare takowane fanni gata ilmin addini Dan kuwa saura kadan ta Haddace alkur,ani mai girma, Sajeeda namatukar son Rukayya kamar yan uwanta na jini haka take jin ta kamar uwa daya uba daya suke ba,abinda Rukayya zata CE tanaso Sajeeda. Batace tana sonsa ba koda kuwa. Baimata ba a duniya inhar kanason kaga. Baccin ran Sajeeda toka taba Yar baiwa haka ma ko a wurin Rukayya batason ko kadan taga yar uwarta cikin damuwa kuma sajeeda bata taba jin haushi ko kyashin Rukayya tafita ilmi ba duk da dai itama tanada nata iya gwargwardo wadan da basu sansuba cewa ma suke yanbiyu ne kasan cewar tun bayan dawowar, Ruky a gidansu Sajeeda Daddy bai taba ban-ban ta musu kayaba kai harta takalmi da sarka iri daya ake saya musu hakan yayiwa mummy dadi sosai yanda Daddy yadauki Ruky kamar sajeeda baya taba nuna wani banbanci duk abinda zai iya yiwa sajeeda to tabbas zai yiwa Rukayyama, duk da yasha samun yan korafe korafe a gurin Abokanansa dakuma wasu amma indai ya fahimci ba maganar arzikice takawo kaba, tun daga ranar kun raba hanya dashi bayason sa 👀 ido Dan yasan duk abinda yayiwa Rukayya Dan Allah yayi kuma yanada tabbacin zaisamu ladansa a gurin Allah . Haka abin yake ko a wurin mummy indai kawayenta suka fara kushe Rukayya nan da nan zata watse mutun komai dangartakar ta dashi kuwa ita a ganinta ko ba ita, ta haifi yar baiwa ba ai Abbanta ciki daya suka fito dashi kuma duk abinda zai cutar da Rukayya bata sonsa Dan tasan duk abinda tayi Dan zumuncine kuma Dan Allah da fatan samun lada a gun Allah. ( Anya a wan nan zamanin zaka iya samun Dan uwanka maisonka da kaunarka saboda Allah kuwa zumuncin yanxu sai a hankali kowa nasa kawai yasani Ya Allah kabamu ikon so da kuma kauna ga yan uwanmu, Ameen ya Ra bbi). Rukayyace zaune a falo tana koyawa su Abdallah home work dinsu Sajeeda kuma na gefe tana Dan duba wani English litreture mummy kuma ta fita da yake yau ba Islamiya kowa na abinda yasa a gaba sallamar Daddyce ta sa kowannensu dago kansa sama Dan amsa sallama Sannu da dawowa Daddy, yauwa yaran Daddy sannunku da gida umman taku har yanxu bata dawo. Bane wan nan zuwa biki haka har yamma tayi gashi inaso muje gidan wani amininah da muka Dade bamu haduba baya kasar jiya yadawo muje muyimai. Barka da dawowa ko bakwaso 😊 sukayi ga aki dayansu Daddy muje basai munjira mummy. Ba kawai cewar Sajeeda yes Daddy kinji Abdallah , no gsky daddy ajira sai mummy tazo inyaso sai mubarshi sai anjima da dare muje Daz my gal shiyasa nake sonki dan kinada hankali ba kamar wadan nan ba Sajeeda ta turo. Baki fadil kuma gwalo yayi mata ta kaimasa doka ya goce ya boye bayan Sister Ruky plzz my sist kice karta dake ni to meye namin gwalo ai nima watarana Daddy zai yabeni bakaman kai ba ko little bro cewa da Abdallah eah hakane Sist kyalesu shida sister Ruky, muma watarana rana sai mun musu gwalo dat my bro oya give me five suka tafa ita dai Ruky murmushi kawai tayi itama tace da fadil leave them kaji sweet.bro dina itama sajeeda ta kwai kwayeta kaji sweet bro dina Ruky ta jefa mata pillown kujera ta gudu ita da Abdallah zuwa daki hmmmm Sajeeda da Ruky kenan everlasting friend Maman Ussee😘 I love you All my fans 💋 🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣2⃣ Maman Ussee😘 Misalin karfe 8:30 mummy da 'ya'yata suka shirya cikin shiga ta alfarma kowansu yaci gayu, Daddy ne ya leko ohh wai haryanxu baku kammala bane koyaya? Nop we r ready kai kadai kawai muje jira OK let go. Gida ne na alfarma Wanda ya amsa sunansa gida, ba karya naira tasha kuka a gidan Dan an zuba dukiya a duk fadin Sama road ba gidan da yakai kayatuwar gidan kai tsaye Daddy cikin gidan ya nufa yayinda mai gadi ya wangale get suka shiga, Wow Aljannar duniya lallai gskyr hausawa ne dasuka CE na zaune baiga gariba habar gidan tamkar a kasar turai duk da dai darene amma tamkar rana saboda hasken lantarki, gefe daya motocine a gibge, an jera su Reras a car pack, sai kuma a center akayi wani Dan round aka shuka flowers ruwa nata bulbulowa kamar korama hasken fitillu ya haske ko,ina ba, cewa komai dayan gefen kuma wurin hutawa ne da kujeru sai rumfa tsayawa na fada muku gayatuwar gdn bannar lokacine, iya haduwa gidan ya hadu sosai kai tsaye car pack Daddy, ya nufa yayi packing, kamin nan suka fito zuwa cikin gidan, Wornder shall never end kunga Fallon gidan kuwa😳 wasu kayatattu. Royal chair's, na hango kai sun hadufa ba karya masu kudi suna sha,aninsu. Gefe guda Dining area ne dauke da wani katon dining table tsarin falon komai red an white ne kai hartama da paint din falorn red ne da white kai nasha kallo fa saura kadan nadan saki layi nadai yi sauri na saita kaina Dan karsu dagoni😜, Daddyne yafara zaunawa tare dasu Abdallah kasan cewar shi ba bako. Bane a gidan in yazo kai tsaye yake shiga ba wani dar dar, mummy kuma tare da Ruky da Sajeeda, Wata matace tashigo da ganinta mai aikin gidance sannuku da zuwa Bari na kira Hajiyar tana sama bawani bata lokaci aka fara cika musu gabansu da cima kala_kala, yayinda kuma Daddy ya daga waya ya sanarda abokinsa isowarsu Dan yasan halin matar gidan inta itane saidai su kwana anan baxata sakko. Ba , Bayan min tuna kadan sai ga shinan ya sakkon mutun mai baiba da kamala ga kwarjini, da murmushi sa ya tarbi abokin nasa ya rungumeshi aka fara gaisuwar yaushe rabo, Alhaji Basheer kenan Amini kuma uban gida a wurin daddy mutun ne mai son mutane kowa nasane yanada daraja Dan Adam baya wulakanta talaka duk Wanda yaxo gunsa zai tarbeshi kamar nasa ga taimako sabanin uwargidansa Hajya kubra macce mai fada ga nuna isa batason talaka ya rabi mijinta Dan ma Alh Basheer na tsaye ne kuma yana takwarata da Allah kadai yasan tsiyar da zata tsula. 'Ya'Yansu shidda Abubakar Umar Usman da Aliyu sai kuma twins Afra&Afnan bayansu bata sake haihuwa. Ba, Abubakar shine babban dansu sai Umar ke bimasa duk da bawata tazarace tsakaninsu ba Usman da Aliyu ma bawani nisa a tsakaninsu, bayan ta haifi Aliyu tadan jima bata sake haihuwa ba har an cire rai sai Allah yabata cikin afra da afnan Alh Basheer yayi murna kwarai da gske kasancewar bashida yara mata duk maza ne adalinlin hakane su Afra suka taso cikin gata sosai ba iyaye bakuma ga yayunsu ba . Bamai takura musu sai abinda sukaso sukeyi tun suna yara abindai ba,a cewa komai idan kanaso kaga fadan Hajya to taba mata yan biyunta ba abinda sukeso a duniyar nan Wanda Hajiyarsu bata musu(Jan kunne👂Hatara iyaye mata mukula sosai da sangarta 'yayanmu dominsu amanace awanjemu ki👉 sani Allah zai tambayeki game da tarbiyar da kika. Baiwa 'yayanki dolene mu tsawatar musu Dan ance kaso naka duniya ta kishi inkaki naka duniya ta soshi haka zancen yake Allah yasa mugane Ameen) Alhaji Basheer rikaken Dan kasuwane kuma shahararren mai kudi Wanda ketashen kudi a wan nan zamani duk da dai ba sa,an daddy. Bane kusan Allah mai hadin zumunta. Wata rana ne Alhaji. Basheer yaje Bank dinda daddy ke aiki domin ya cire wasu kudade nashi sai aka samu akasi bai samu yanda yakeso ba kuma gashi tafiya zai yi yarasa mafita shine daddy ya taimakesa yasamu kudin iya adadin abinda yakeso to tun daga ranar yazama duk indai kudi yakeso a bank dinsu Daddy to Daddyn kawai zai nema hartakai ma daddy da kansa ya sha kawoma Alhaji Basheer kudi har gida wan ne yasa sukayi sabo har Alhaji Basheer yakan Dan saka daddy wani abu Wanda yake na sirri kuma ayimasa yanda yakeso batare da ansha wahalaba wan nanne dangantakar Daddy dakuma Alhaji Basheer , Bayan sun gaggaisa Ruky da Sajeedama suka gaida shi cikin girmamawa, sosai yaran suka bashi sha,awa ya yaba da hankalinsu sosai har yake tambayarsu ajinsu nawa da skull dinda suke suka bashi amsa kai tsaye ya CE gaskya kunada kokari so keep it up duk Kansu dariya sukayi sukace Insha Allah , Jim kadan sai ga Hajya Kubra manta manta anfito ana wani tako daya bayan daya kamar,batason taka kasa tana wani nuna is a ,daga saman stairs falon ta nufa gurin da su Daddy ke zaune anata labaran duniya shida Alh su mummy kuwa hankalinsu nakan palasma TV dake jikin bango suna kallon news. Au Alhaji wai baki mukayine,murmushin taikaici yayi, yana mai jinjina hali irin na matarsa , Eah kawai yace mata yaci gaba da abinda ke gabansa . Sannuku kawai tace dasu takoma warta dama ko sakowarda da tayi taga Alhaji ya matsa mata da kirane shine ta sakko taga meyene gaidata su Sajeeda suka shiga yi a dakile ta amsa tayi ficewarta Alhaji baiji dadin abinda tayi ba ammato ya ya iya. Wuraren 10:30pm suka yima Alhaji Basheer sallama ya dauki kudi yabasu sukaki karba aikuwa yayi juyin duniya sukaki saida yanuna bacin ransa kamin nan, daddy ya umurcesu dasu karba kishi Sajeeda CE ta amsa Ruky kam ki tayi saboda kunya. Muje zuwa Maman Ussee😘 Kuyi hkri aiki ne yamin yawa shiyasa but insha Allah gobe zanyi mai yawa nagode sosai masoyanah🙏 🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣3⃣ Maman Ussee Da isarsu gida kowa, yanufi dakinsa Dan kwantawa, a huta yaukam ba, zancen fira , Ruky da Sajeeda wanka kawai sukayi sai alwala kowacce ta nemi shifida, sai. Bacci Kashe gari tun safe suka tashi bayan sun kammala ayunkan gida kai, tsaye dakin mummy suka, nufa bayan sun gaidata da. Ne , Suka nufi dakin daddyn su, shima sukayi gaidashi, kamin nan sukaje suka ci gaba da sauran yan aikace aikacen gida Dan mummy bata barinsu girki saidai ta nuna musu amma har yau bata sake musu girki ba acewarta su yarana har, Yanxu baza ta sake musu komai ba, sai nan gaba iya kacinsu shara sai wanke wanke , da sauran Dan abinda , baza,a rasa ba. Time din break nayi kowa ya halara mummy tayi saving din kowa, aka fara cin abinci , bayan an kammala ne Daddy ya ke tambayar su daya bayan daya koda matsala ne Dan, Dama haka yakeyiwa kowa. Daga nan duk mai bukatar wani abu saiya fada kowa yace , Bakomai Daddy ya wuce zuwa Bank. Dan yau ba skull ana hutun good Friday ne yaran yau basa zuwa skull , Bayan sun kamala aikinsu sai suka tambayi mummynsu sunaso, ne suje dubo wata yar class dinsu datake, nan unguwarsu . mum tace dasu karsu Dade suyi sauri su dawo , tau suka amsa kamin nan suka dauki hijabs dinsu, Suka ficce daga gidan , gidansu Hafsat suka nufa nan ne bayan layinsu da sallamar su suka shiga cikin gidan, bayan sun gaida umman Hafsat sai suka shiga dakin Hafsat din, bayan yan gaishe gaishe , suka fara fira irin nasu na yan makaranta, Basu suka dawo ba sai bayan an taso daga salar jumma,a dayake yau Friday ne , kai tsaye gida suka nufa koda sukaje mummy tayi baki bayan sun gaida sar da bakin mummy dakin su suka shiga suka sayi sallah bayan sun kammala, suka fito suka Debi abincinsu suka koma dakin su, sunata wasa da dariya batare da wata damuwaba yan biyun mummy kenan!!! Maman Ussee😘 Note Dan Allah kuyi hkr wllhi kwana biyu bana jin dadin ne amma yanxu naji sauki zanci gaba dayi muku insha Allah nagode sosai da kulawarku💯 🙎 YAR BAIWAH🙎1⃣4⃣ Maman Ussee Safiyar Talata tun safe suka tashi suka fara shirye 2 na zuwa skull, bayan sun kammala da komai da komai Daddynsu yadaukesu yakaisu bayan ya ajiyesu sai ya ficce zuwa wurin, aikinsa Su Abdallah da Fadil ma nasu bangaren suka nufa, yayinda Sajeeda da Rukayya, suma suka wuce, zuwa assembly, ground, After ankare Assembly duk student's suka ficce, zuwa classes dinsu Dan daukar darasi, bayan Class master din su Ruky yashigo ya kira register, sai aka fara gabatar musu da lesson din nasu . Kwanci tashi baya hana zuwa yau har su Sajeeda da Rukayya sun rubuta JSCE lafiya lau murna gurin Daddy da Mummy kamar me, Haka Rayuwarsu taci gaba da kasancewa har lokacin da exams dinsu ya fito Daddy yayi musu alkawarin zai canja musu skull dan ya yaba da kokarin yaran yayinda Alhaji Basheer shima yayi alkawarin zai bada nasa contribution, din idan zasuje gaba Dan shima yaran suna birgesa, more especially Tarbiyarsu ga girmama nagaba dasu, Kamin karshe Hutu Daddy yakai Rukayya da Sajeeda Raba domin suyi hutunsu acan , sunsha Hutu kam Dan saida sukayi kusan wata Daya acan ba karamin Dadi hakan yayima Baaba Dan tana matukar son Rukayya , bayan sun dawo, Hutu kuma sai suka dukkufa zuwa Islamiya Dan dama sauran kadan su sauke kuma Daddy yayi musu alkawarin sai sun sauka zai kaisu SS one Dan dama hakan sukeso badan ma sunje Hutu a Raba ba da yanxu sun sauke hakan sukeyi kullun akaci sa,a kuwa Rukayyace ta fara sauka bayan Sati daya Sajeeda ma tasauke Murna da Daddy yayi. Bata misaltuwa kullun saiyayiwa yaran sa addu,a Allah yakara musu basira Alhmdllh Addu,arsa ta karbu Dan kuwa ga sakamakon hakan yagani. A tare daddy ya hada musu walimar sauka a gida bayan an gabatar musu da wata walimar a makaranta, ba laifi kam an taru bayan an gabatarda yan naseehohi akayi musu addu,a sai yan kayan rabo da akayi bayan an rufe taro da addu,a kowa ya watse, Daddy ne zaune da yaran sa anata wasa da dariya uhuum Abban yara wai mexai hana ka kokarta ka kai su Iman ne naga can ana karatu sosai ko cewar mummy Daddy ya nisa eah haka ne amma kudin ne , sunyi yawa kuma nafiso nakaisu Inda zasuci gaba da Hadda Dan ,dama nayi shawara zan kaisu, Sultan Abubakar Maccido Islamic college, koya kika gani ,ai Ruky da Sajeeda najin haka su fara murna yeee Thanks much Daddy we love u Daddy Allah yakara budi sukaje suka Rungume Daddyn nasu suna murna ,daga nan kuma aka ci gaba da hirar duniya kamin time din sallar magrib yayi , Dad yaja su Fadil zuwa masallaci yayinda su Sajeeda da Rukukayya suka shiga cikin dakin su domin gabatar da Sallar magri b. Bayan kwana biyu Daddy yadaukeso sai new skull dinsu dayake akwai masu yin day a ciki akwai kuma masu yin boarding Daddy baya da Ra,ayin barinsu suyi boarding, Day yasaka su bayan ya yayi musu registration, da duk wani abubuwa da yakamata sanda akayi musu interview, aka basu classes saidai ba,a ajesu a class daya ba kamar yanda sukeso , badan ransu yaso ba,haka suka hakura Dan bayanda zasuyi, haka suka zauna a new skull din taso dayake akwai Dan banbanci kadan Dan yanxu sai 4:pm suke tashi dan, skull din hade take da Islamiya Ruky da Sajeeda baruwansu dashiga harkan da banasu ba hakan cema tasa basuyi wasu sabbin kawayewa ba Dan acewarsu kowa ya tsaya matsayin sa Inda Allah ya ajesa , kwana biyu sukayi suna a cikin makaranta akan BAIWAR Ilmin da Allah yayi musu abin sai Wanda yagani Teachers suka fara sonsu duk Inda kaji cikin skull zance Sajeeda da Ruky akeyi Abin yafara bawa wasu student's din haushi Dan yanxu da wuya ayi wani skull conpotiong ba dasu ba gasu da kyau kamar diyan laraba da yawa ss3 student, sun sha musu gargardi akan wasu malaman, abin har mmki yake baiwa su Ruky Dan su a tsarin su ba soyayya a halin yanxu Dan Daddy baya barinsu ko da wasa balantana ma a skull dayake dokar makaranta CE . Maman Ussee😘 🙎 YAR BAIWAH 🙎 1⃣5⃣ Maman Ussee😘 Sajeeda da Rukayya yaran kirki, wadanda bazaka taba cewa sun tsokaneka ba , zaune suke a harabar, area class, sun duba wani book, dukadai ne zaune a gurin sai wadan da. Baza,a rasa ba, Sajeeda ta kalli Rukayya, yadai Sist naga ki wani iri neyake faruwane. Murmushin karfin Hali kawai yar baiwa tayi, Mekigani ne hln ba komai, nikuma dadina dake shegen zurfin ciki yanxu akwai abinda yake damunki a duniyar nan dabaza ki iya fada mun shi ba, koda yake ,may be kinada , Wata wadda ya dace kiyi sharing din fillings dinki da ita wadda ta wuce ne, nakula dake tun jiya bakya jin dadi but saboda, karfin hali irin naki nayi ta tambayar ki amma kin ki, fada , Namiki alwarin yau idan har baki gaya min. Ba to damunje gida nikuma sai na gayawa ,mummy ita ai dolenki, ne ki fada mata 😳 zaro ido Rukayya tayi hadi dacewa hava Sist kin kasa fahinmta ta. Kawai ne nagaya miki am OK , Kawai dai na tuna da Raba ne shiyasa hmmm Rukayya yaushe kika koyi karya nidai nasan wllhi dakwai wani abin da kike boyewa kuma zan gyaleki. Baxan sake tambayar ki. Ba amma nima wata rana ko kin gani cikin damuwa to karki kuskura kice wai zaki tambayeni meke damuna, Dan ba fada miki zanyi ba ta tashi fuu da dauki sauran tarkacenta ta kara gaba, dafe kanta Rukayya tayi Dan batasan ya zatayi da fushin Sajeeda ba , Tana matukar son 'yar uwarta. To amma tayaya zata iya fada mata wan nan abun ai sirrin ta ne. Bedace sai Sajeeda taji ba duk da yake tana fuskantar yan matsaloli Kadan amma tayi alkawarin ko mummy. Baxata fadamawa ba Dan ita kunyama takeji ace wai girma yazo mata duka duka shekarunta nawa yanxu 15 ne fa am still young ta furta a filli yayinda tayi wani Kayataccen, murmushi, 😊 bara naje nayi bikon my Sajeeda yar rigama nidai maman Ussee, gefe. Nakoma nasha 😀😀😀😀 dariya ta mai isana kamin nan nace su Rukayya manyan mata girma yazo kenan🙊 ba,aso a fada a gida lol. Duk abinda sukeyi akan Idon sane yakasa jure taya zai iya hakura da Rukayya da dinbin so da kaunar da yake yimata kuma da kunya yaje yasameta da sunan wai yana, sonta yarinyar karamace batasan meye so ba but zai yita renon Soyayyar ta a cikin zuciyarsa har sai nan gaba kadan ya fada mata dama duk wani move nata akan Idinsa ne bashida wani aiki sai na kallon ta a duk fadin skull din. Baiga wata ya macce wadda zai iya , baiwa zuciyarsa ba kamar Rukayya tun farkon kasu su ,skull din yake masifar sonta duk ,da dibin yanmatan da ke zarya a gd da kuma waje shi baiga wadda tayi masa ba irin Rukayyah Ring bell din da yaji ne yadawo dashi daga Duniyar tunaninda ya tafi Dan zuwa yayi musu lesson dama da an dawo daga break, yanada class dinsu cikin sauri ya kwashi abinda zai bukata yakara gaba . Towai waye wan nan🤔 Bakowa bane ila uncle Faruq yaro mai ki da kansa ga kyau ga ilmi uwa uba ga kudi bayason raini ,kokadan bai cika damuwa da abinda be shafesa ba duk da iyayensa nada kudi. Bedamu da nasu ba yafi bukatar tasa dukiyar gumin kansa , mahaifinshi ,yanada kudi ba kasan. Ba Amma Faruuq basune gabansa ,ba bayan dawowarsa daga maleshia karutu shine yanema kansa aikin koyarwa a S A M I C duk da wurare da yawa, ana Bukatar sa . Amma shi duk bayasonsu ,yafiso. Ra,ayinsa , Saigashi kuma Allah ya jarabceshi da son wacce batama San yana yi ba hmmmm duniya kenan. Rukayya Bata fice Class dinsu ba saida ta fara zuwa gurin yar uwarta Sajeeda tabata hkr dayake kunsan Sajeeda da Rukayya sai Allah nan da nan a shirya sukaci gaba da wasansu da dariya Ring din bell ne yadawo dasu Rukayya tacema Sajeeda Sist bara na wuce Dan wllhi Uncle Faruq ba mutunci ne dashi ba zai iya hanamin shiga class idan har yarigani kuma. ,baya latti yanxu haka in ance yana hanya bana musu , to sarkin tsoro fara gudu tundaga nan suka kwashe da dariya su duka Ruky ta kama Banyan zuwa Class dinsu har ta kusa kai ta tuna da book dinta yana hannu Sajeeda dazu ta ficce dashi kuma Uncle Faruq yabasu assnmnt yaune kuma ranar dubawa da gudunta ,ta koma baya sai Class dinsu Sajeeda Sist ban note Book dina na Geography, dakika dauko dazu , cikin sauri ta karba ta nufi hanyar class dinsu saidai tayi rashin sa,a Dan kuwa har yariga yashiga 😳 zare ido tayi hadi da Dora hannu aka🙆 nashiga ukku yauni Rukayyatu , wan nan Uncle din mai disga mutane yaxanyi dashi ,bayan ta saita kanta kawai tayi shahada tace excuse me sir yes ya amsa batare da ya juyo ya kalli me magana ,ba duk da yasan ko wacece, am sorry nayi late wallahi na manta note book dina ne a class dinsu YAR uwata koda naje na karbo harkashigo kayi hkr plzz, baice da ita kalla ba saida yagama rubutu a white bord kamin nan ya juyu ya kalleta in serious student taya za,ayi kibar note book dinki a hannu wata inhar yanada muhimnanci a tare dake bari kiji u wll not attend my lesson kuma ki bacce min da gani kina disturbing , dinmu hkr tashiga bashi kamar tayi kuka ,amma ko kulatama beyi ba haka ta karashi tsayuwarta takoma bakin class ta zauna, yayinda shi kuma a cikin Ransa yake cewa am sorry my Angel bansan ya zanmiki ba shiyasa namiki hakan. Maman Ussee😘 🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣6⃣ Maman Ussee😘 Gefen Rukayya takoma tana duba book dinta ,yayinda uncle Faruq yaci gaba da lesson Sometimes yakan Dan , dubeta duk da dai baya ganin fuskarta ,amma yana ganinta a zaune wani ,nishadi yakeji idan har yaganta , bayan. Yakare lesson dinsa yana fitowa cemata kawai yayi ke biyoni muje ki karbo sauran note book din yan class ,dinku kisameni a staff room ko dago kai batayi ba ,balantana ma ta bashi amsa saida ya sake maimata kiran ta ke Rukayya bakyajina double funishment, sai nasa distilling, master yakoya miki hankali ,a sanyaye, tace sorry uncle wllhi banji bane ina kara2 ne kuma ta duk ji kawai dai, yabata haushi ne yasakata zaman 30mnt a waje kuma yamata hasarar daukar lesson dinta ,gashi harda wani CE mata ke danya raina mata wayyo ,bayan ta basa hkri ne tashiga class ta hada books din yan ajin nasu guri ,ta fita bata zarce ko,ina ba ,sai staff room. Dashigarta kai tsaye , teburinsa ,taje ta Dora books din bayan ta sake. Basa hkr baice da ita komai. Ba kawai dai yana kisima kyau da kuma sweet voice dinta hardai dayake cewa kayi Hkr uncle jiyake kamar ya rungumeta hardai inta bude idonta masu kara tafiya da imanin sa, da kyar yasamu ya saita kansa cikin voice sarkake yace da ita u can go but karki sake maimata hanka kinjiko ta amsa da to kawai tayi ficewarta , shi kuma gogan tunanin yanda zai iya bullowa Ruky kawai yake yakasa Dan besan yazata karbi zance nasa ba. Kai tsaye class dinsu ta nufa cike dajin haushi uncle Faruq sai wani tasata a gaba yayi yana kallon ta da wasu mayyun idonsa kawai ya hanata samun abinda tazo nema akan wani ka,ida nasa na banxa ,to na banxa mana cewar Rukayya ai nabasa hkr amma yakasa ganewa, tana shiga sai ga wasu yan SS3 student prefect sun shigo class din bayan kowacce , student ta nutsu suna wani yatsina Ku wayece dazu mukaga tabi ,uncle Faruq a cikinku Ruky ta yi shuru kowama baiyi magana ba ,Ku wai ba . Magana ake muku bane kun maida , mutane wasu yan iska , can sai wata ta nuna Rukayya Sisters wan Nance , kan uban chan, shine Dan rainin wayo kinaji ana magana kin yima mutane shuru to biyomu, 🙆 Rukayya tafara magiyar rokonsu ,amma Sam suka dage saita biyo,su Ba yanda ta iya dolenta ta bisu , sanda suka gama disgata kamin nan suka bata punishment, din wankin , toilet kai ranar Rukayyatu taga bala,i ,iri iri duk sanadiyar uncle Faruq akan wai su sonsa sukeyi kuma suna zargin Rukayya ma wai ,sonsa take basu, San ita yanxu kara dasa tsanar sama sukayi a zuciyarta ,baita takoma ,class ba sanda akaje shot break gashi dama bata jin dadin jikinta maranta ke ciyo gakuma wani azababben ciyon kai. Sajeeda CE tashigo class din tayi mmki sosai dataga Ruky a saman decks, tanata barcin wahala Dan yau ta bautu, Shafa fuskarta Sajeeda tayi sleeping beauty kintashi muje short.Break ,tadanji jikin Ruky da zafi nan daban , Sajeeda ta rude Sist meya faru tafara jijjigata Ruky ta bude idonta da kyar saboda zafinda suke mata Sist bana jin dadine muje, Ki kaini skull clinic itace ta taimaka mata har zuwa clinic din. Bayan Norse ta dubata ,saita. Bata magani kamin ,nan bacci yadauketa Sajeeda ta kwantar da ita akan bed din clinic cike da tausayi takoma Class dinsu. Maman Ussee😘 Nagode sosai my fans😊 🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣7⃣ Maman Ussee😘 Rukayya bata farka ba sai guraren 2:pm koda ta tashi ba,inada ke mata ciwo saidai kawai batajin kuxazari ,a jikinta hakan, dai ta kejinta fayau da ita ,uncle Faruq yasha Allah ya isa kamar me a gurin Ruky Nurse CE ta taimaka ,ta gyara jikinta kamin nan tafito a jima anjima takan yi tsaki kadan., Jefi jefi acinkin zuciyarta kuma cewa takeyi wllhi baxan. Taba yafewa Uncle Faruuq ba Dan duk shine silar shiga ta damuwar da nake ciki a yanxu haka kurum Dan mugunta ,yahanani shiga class gashi yau ban fahimci komai da akayi ba yamin hasarar the whole day mugu kawai bantaba jin na tsani wani mutun ba kamar kai. I Hate u, I hate u, I hate u ,uncle faruuq wasu hawayene suka fara wanke mata fuska kwata kwata yau ji take kamar ta kashe Faruuq Dan duk shine sanadin komai da yafaru da ita ko a gidansu bata taba irin wan nan wahalarba sai gashi yau ansaka wankin toilet shidda ita kadan ta , ga maranta dayake mata ciyo kadan kadan rumtse ido tayi ta sake budewa yasake maimaita Wllhi baxan taba yafema ba wannan cutuwar, A bangaren faruuq kuma tun bayan tafiyar Rukayya tunanin ta kawai ya adabeshi book dinta ya dauko ya rungumeshi ki yake ,kamar ita din CE a hankali ya fara gutta I LOVE YOU SO MUCH, My Angel, ya sumbaci book din kamin nan ya hada sauran book din ya aje a cikin locker din Decks, din sa ya dauki na Ruky ya fita dashi gabaki daya ma skull, din yabari, Sajeeda kuwa lesson ake amma bata fahimtar komai ,duk hankalinta yana gun YAR uwarta Dan batasan a wane hali takeba Allah Sarki Sajeeda ta Rukayya ,da kyar taga karfe 2 Dan ma a hana su fita sai anyi sallar Azzahar kawai dai Sajeeda ji take kamar ta daura hannu aka ta kwala ihu Dan jitake kamar ciwon Rukayya yadawo jikinta batasan ya mummy zata dauke ta ba, idan har ta gane Ruky batada lfy gashi bata samu damar zuwa clinic ba ,haka ta hkra sai guraren 4 haka taje ta dauko Rukayya a clinic suka shiga skull bus sai gida, Da shigarsu gida mummy ta tarbesu Dan taga Sajeeda CE ta riko Rukayya wadda ciwon ya kara tashi da kyar ma take gani dishi 2 take gani subahanallah Yaran Daddy lafiya dai meyake faruwa wani Abu aka muku ne Sajeeda ko kamar jira take mummy tayi magana saita fashe da kuka , ke lafiya meyasamu Rukayyarne, kike kuka yi shuru gayamin meyake faruwa ne, mummy Rukayya batada lfy yau gabaki daya a clinic ta wuni , Taslima mummy tashiga yi kamin nan ta dafa jikin Rukayya taji zafi rau ba bata ,lokaci tayima Daddy waya take sanar dashi halin da ake ciki ,batare da wani bata lokaci ba sai gashi.Nan yadawo ,daukar Rukayya yayi yasaka ta a mota shida mummy, suka kaita asibiti Sajeeda kuma aka barta gida ita dasu fadil da Abdallah kuka kawai takeyi Fadil ne me tambayar ta Sister meya faru da Sister Rukayyahnah naga an dauke ta cikin shashekan kuka tace batada lfy ne Fadil kuyimata addu,a Allah yabata lfy cikin gaggawa Ameen suka amsa kamin nan suka wuce dakin su kowa ba dadi a ransa ,suna taya Yar uwarsu jimami (Ya Allah kabamu Ikon so da kuma kaunar Yan uwanmu tsakani da Allah da zuciya daya) Daddy bai zarce ko,inaba sai specialist. Hospital da zuwansu bada wani bata lokaci ba aka karbi su yayinda aka shiga baiwa Rukayya taimakon gaggawa , Daddy hankalinsa a tashe sai dama kinsan Rukayya batada lfy shine kika kasa gayamin, to akan wane dalili, sorry Abban yara wllhi bansan cewa batada lfy ba kasan bayanda za,ayi na sani ban gayamaka ba kawai dai irin zurfin cikintane bata fadaba cewar mummy Daddy yanada zaune yakasa tsaye ko kadan bsyason abinda zai taba lafiyar yar mutane saboda ita amanace a gurin sa , yayi alkawarin zai kula da ita kamar yanda zai kula da 'ya'yansa da ya Haifa gashi Rukayya tasamu rashin lfy baima sani ba sai yanxu, shi duk laifin mummy yake gani Dan tafisa kusanci da su to meyasa bata fadamasa ba tun wuri sai. Bayan Abu ya zama whose Maman Uzuwa😘 Muje zuwa!!! 🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣8⃣ Maman Ussee😘 Doctor ne ya fito daga room dinda aka ajeyi Rukayya , Daddy ya tarbesa cikin hanzari yadai likita ,cemasa kawai yayi ya biyosa zuwa office din sa, batare dawani bata lokaci ba yabi bayansa mummy kuma Room dinda Rukayya take ciki ta shiga koda tashiga ganin Rukayya tayi kwance abinta sai sharar bacci takeyi ana mata karin ruwa, Tausayintane ya kama , Allah sarki Baby Ruky Ashe bakida lafiya shine kikaki fada min har sanda Abu yayi tsanini ban kyau taba daban gano cewa , ur not felling too well ba but I promiss daga ,yau zan kara himma wajen kula dake banason ko kadan wani Abu yasameki Rukayya Allah yabaki lfy , ta sa hannu ta Shafa fuskarta mai haske , Abangaren daddy kuma bayan yashiga office din Doctor ya zauna, Doctor yamaida hankalinsa a gurin daddy Dama ba wani dogon matsala bace kawai dai tasha wahala ne matuka watakilla ko ansaka wani aiki ne mai wahala or something, like that kuma ga period, dinta yafara zuwa da ciyon Mara Wanda duk shine yakara tsanata akan yawan. Dukin da tayi tayi that why yasaka mata fever Dan jinin bai sauko, a gurin. Da yakamata ba but Insha Allah she wll soon be fine, yanxu tana bukatar Hutu nayi mata aluran bacci Insha Allah koda zata tashi ba wata damuwa kawai dai a kiyaye gaba Dan gudun faruwar irin hakan,saboda worm dinta bayada karfin. Da juriyar daukar wahala sosai irin hakan nan, Ajiyar zuciya Daddy yayi kamin nan ya yima Doctor godiya yakarbi takardar magani Dan yaje yasayo, ******* ******* ******* A gida kuwa Sajeeda banda aikin kuka ba abinda takeyi su Fadil ke Rarrashinta hankalinta duk yakasa kwanciya, ganin har 6 :pm ba mummy kuma ba Daddy gashi ita. Ba wayace da ita. Ba balantana, takira taji ko lfy duk ta rude ta kasa aikata komai tunanin, a wane hali yar uwarta take a ciki kawai takeyi jitake, kamar ta dawo da ciyon yadawo kanta, tun daworsu har yanxu uniform, ne a jikinta , takasa cirewa ko Islamiya ma yau. Ba Wanda yaje a cikin su gidan yayi quit sosai, ba dadi su Abdallah ma haka suka yita bata hkr amma, takasa daina kuka shigewarsu sukayi nasu dakin kowa yayi jugum, Mummy na zaune ita da Rukayya daketa barci daddy yashigo, da ledar magani an rubuta NATA Benji Pharmacy, Ajewa yayi ya zauna akan kujera yafara jeroma mummy question , kinasa Rukayya aiki mai wahala ne? Meyasa baki fada min batada lfyba saida Abu yayi tsanari? Dama kinsan batada lfya Amma shine baki badaminba? Wane aikine kikasa ka Rukayya mai wahala a yau? Answer me , Sukuyarda kanta tayi kasa tafara bude baki Daddyn Yara wllhi bansan cewa Rukayya batada lfya ba kaima sanin kanka ne lfy lau muka rabu da ita dazu da safe ,aiki kuma ni banda shara da wanke wanke ba abinda suke min a gida yauma ba abinda sukayi da dawowarsu daga school ne fa nakiraka a waya Dan Sajeeda CE ta shigo da Rukayya ko tafiya ma bata iyayi kawai dai mujira farka warta sai mutanbayeta ko dakwai wani mai takura matane bamu sani ba, It's OK Allah yabata lfy kinga an kusa magrib zanje gida na duba su Sajeeda sai na taho muku da sauran kayan bukata Dan nasan maybe nan zaku kwana, badamuwa mummy ta amsa . Da zuwansa gida car kawai ya ajeye ya fada masallaci Dan ya gabatar da sallah, bayan yakarene yashiga cikin gidan , bakowa a Fallon kiran sunanta yafara yi a Hankali Sajeeda, Sajeeda , naam ta amsa cikin sanyi ta fito INA k'annen naki , Daddy inaga sun tafi masallaci OK to ki kwantar da hankalinki sister dinki taji sauki sosai ki je dakin mummy dinku kidauko , blanket da kayan ta ki hada harda na Rukayya ki dauko cups da spoon da flalet, kinji ki dauro Ruwan zafi ki saka a Flak's kamin nayi wanka kin shirya komai sai muje hospital, din Ku dubu Rukayya kinji To ta ansa kamin nan ta fara hada abinda aka umurceta tayi guri daya , Basu bar gidan ba sai bayan Isha ,saida Daddy yafara biyawa super market ,ya sayo musu kayan tea kamin nan ya biya restaurant, yayi musu take away, Basu zarce ko INA ba sai a ,Asibiti, Daddy ya dauko sauran kaya yayinda Sajeeda dasu Abdallah suka dauko saura, Room dinda aka kwantar da Rukayya nan suka shiga sai dai har yanxu bata farkaba Sajeeda da gudu ta isa bakin gadon ta k'amk'ame ta tana Hawaye Mummy CE ta CE ke lfyarki kuwa inkinka jimata ciwo fa kin wani riketa kamar saceta za,ayi shikuma Daddy tausayinsu yagani kasancewar yasan yanda suka shaku da junansu , Cikin bacci Rukayya taji kamar an riketa bude ido tafarayi tana gani bishi bishi kamin idonta suka bude fabaki daya, ta kalli Sajeeda Sist meya faru dani Inane nan, Daddy ne ya dafa kanta sorry Babynah nan Asibitine bakyada lfya ne shine muka kawo ki hpe dai bawata damuwa ko eah ta amsa yayinda tashiga tunanin abinda Yafaru da ita dazu tsaki taja a cikin zuciyar ta sake cewa mugu kawai saida yayi sanadin kwanciyata asibiti Allah ya isana mummy CE ta taimaka mata tashiga toilet ta gyara kanta duk kunya ta isheta bayan ta canja kaya mummy ta hada mata tea mai kauri ta mika mata tasha sai Sajeeda ta dauko Take away tafara bata a baki tanaci kadan kadan tanajin dadin kasancewa tare da family dinta Dan soyayyar da suke nuna mata shiyasa a kullun sai tayi musu addu,ar gamawa da duniya Lafeeya. Maman Ussee😘 🙎 YAR BAIWAH 🙎1⃣9⃣ Maman Ussee Sajeeda saida ta fahimci Rukayya tashi dayawa San nan ta daina bata abinci sun Dan taba fira , anata wasa da dariya Daddy ya kalli Rukayya, yadai baby tazu aikin meye kikayi mai wahala ne a gida ko a skull, Dam taji gabanta yafadi runtse ido tayi ta tuno da irin azabar da tasha a gurin su Sister Jameela Budurwar uncle Faruuq, sake bude ido tayi nanda nan mood dinta ya canja, gabaki daya fara,ar ta. Ta dauke murmushin karfin hali tayi sannan tace bakomai Daddy bayaso ya takura ta duk da ya fahimci dakwai wani Abu amma bayaso yayi forcing, dinta dole saita fada basar da zancen akayi aka dauko wani zancen na daban, Basubar asibitin ba sai guraren 10:30pm ya dauki su Sajeeda da Abdallah da Fadil zuwa gida yayinda aka bar mummy ta kwana da Rukayya kamin gobe su nemi sallama, Sajeeda ma ba,ason ranta ta tafi ba Dan dai Daddy yace gobe dakwai zuwa skull kuma bai dace Dan Rukayya batada lfy Sajeeda taki zuwa makaranta ba dolene ita taje , Bayan sun tafi. Mummy ta dubi yarta tafara yimata nasihohi Dan ta kula da kanta, da abubuwan da duk suka dace uwa ta fadawa yarta wasu Rukayya saidai ta sunkuyar da kanta kasa Dan kunya takeji mummy sai dai tayi murmurshi , Dan tasan Insha Allah irin tarbiyar da suka baiwa yaran su da wuya su fandare inba wani ikon Allah ba kuma tana musu fatan samun kariya da duk wani sharin mai Sharri, Kashe gari tun safe Sajeeda ta tashi tashirya cikin uniform dinta, tanata jin wani iri Dan ta Riga yasa ba da komai a tare sukeyi da yar uwarta Rukayya sabanin yau da ita kadai takeyin komai sabo kenan turken wawa. Bayan Daddy ya ajiyesu a skull saida yabiya office din principal yayi report, cewa Rukayya batada lfy sai dai next week zata fara shigo wa insha Allah da yake ranar laraba ne abin yafaru gashi kuma yau alhamis da yau da gobe baxata shiga ba Dan assabar da lahadi week end ne sai dai on monday , principal din yace it's OK badamuwa Allah yabata lfy sai dai on Monday din nan tashigo saboda sun fara texts kar tayi missing Dan nasan yar wajenka she's very hard working student Daddy yaji dadi sosai ya basa hannu sukayi misabaha kamin nan ya fice daga skull din, zuwa Hospital Dan ya dubo ya jikin na Rukayyatu. A asibiti kuwa bayan Doctor ya duba ta da safe. Ba wata matsala sai ya rubuta musu sallama kuma ya umurci data sha maganin ta abisa ka,ida kuma cikin lokaci, Daddy kawai dama suke jira yazo su wuce da isuwarsa daukansu kawai yayi bayan yayima Rukayya ya jiki ya kwashesu sai gida daga nan kuma ya ficewarsa zuwa gurin aikinsa, Faruuq ne yafito daga cikin motarsa kiran Mercedes sanye da Riga da wando na jeans wandon. Baki Riga kuma fara anyi mata rubuta da bakaken harufa an rubuta it's my Time bai zarce ko,inaba sai admin block yaje yayi sing kamin nan ya wuce staff office ya dauki abinda zai dauka ya nufi class dinda yakeda lesson wato A class SS one A ajin su Rukayya a zuciyarsa muradin ganinta kawai yakeyi Dan tun jiya yakejin faduwar gaba gani yake kamar wani Abu yafaru da ita bayan sun rabu jiya dashigarsa, bayan student sun gama gaidasa Sit dinda take zama ya kalla amma ga mmkin sa ba tanan sake ,daga Kansa yayi ya kalli wurin bayaso ya tambayi yan class dinsu Dan kar suyi suspecting din wani Abu ,haka dai ya daure ya fara lesson din zuciyarsa sai zafi take baiga Angel dinsa ba, wata dubara CE ta fado masa arai dayake jiya books din su, yana hannu sa shine yayi amfani da wan nan damar ya aiki class captain Dan taje staff room ta dauko books din tanan zai San in angel dinsa na nan ko bata nan bayan ta kawo yafara mark yana kiran suna Dan mai littafi yazo yakarbi kayansa , da haka har yakai ga nata yakira name dinta Rukayya Sa,eed shuru ba Wanda ya karba ,saida ya maimata har sau 2 . Kamin nan yan class dinsu ka CE uncle yau batazoba ,what? Yafada adan razane sai dai a hankali yayi kokarin saita kansa kamin. Nan yace saboda meye batazoba yau muma bamu sani ba suka. Bashi amsa daga baya sukace akwai dai sister dinta a C class sai in ita za,a tambaya cewa kawai yayi suje su kirata member dayace cikin yan Class din taje block dinsu Sajeeda danyin kiranta bayan tazo, uncle Faruuq yakalleta ke INA sister dinki meya hanata zuwa skull yau , uncle batada lafeeya kuma whorse Dan yanxu haka tana asibiti ,Dam Dam Dam yaji gabansa ya fara duka acikin ransa cewa yake to meke damun my angle yazama wajibi naje naganta to amma ta yaya zanje? A wane matsayin? Ganin zai batawa kansa lokacine yasa ya. Baiwa sajeeda book din Rukayya tare dayi mata fatan samun sauki ya tambayi Sajeeda a wane asibiti ne aka kaita specialist kawai tabasa amsa ta juya zuwa class dinsu Dan daukar lesson dinta. Maman Ussee😘 Naga sakonku my fans INA godiya sosai da kulawarku👍 🙎 YAR BAIWAH 🙎2⃣0⃣ Maman Ussee😘 A gurguje ya kammala duk wani abinda yakeyi yaje yadauki excuse, bai zame a ko,inaba sai a specialist hospital, room by room yayita shiga amma komai alamarta baiganiba kamar ya daura hannu aka yayi ihu meyasamu Angel ya akayi bansaniba anya zan iya jure rashin ganinta kodai naje na tambayi sister dinta gidansu, ohh no baxan iyaba banaso ,ta fahimci wani Abu a halin yanxu she's still young, batasan meye so ba shikadai yaketa sambatunsa , jiyake zuciyarsa kamar zata faso kirjinsa ta fito in bai samu Rukayya ba ohh wai meyake faruwa dani ne young girl tanata wahalad dani abanxa batama San inayiba, car dinshi ya shiga ya tadata ya bata wuta sosai sai gida haka shima yakejin kansa kamar bashida lfy har mamakin Kansa yakeyi ,wai yarinyarda bata wuce 15 ba take rudashi ,haka yaga mata kala2 amma baitabajin wani fillings akansu. Ba sai ita, ita din daice a cikin zuciyarsa!! A katon Falon gidansu ya zube. Dafe da kansa , ya Dade yana zaune a gurin yanata tunanin ,yanda zai bullo wa lamarin Dafa shi yaji anyi, a hankali ya dago Kansa yayansa yagani yadai Umar lafiya kake kuwa naga kayi zurfi inata sallama bakajiba, Haka dai naganshi kwanan nan bai cika son surutu ba dama shi bai faye magana. Ba amma kwanan, nan abin yayi whorse cewar Hajiyarsu dago Kansu sukayi a tare suka gaida mahaifiyar tasu , cikin girmamawa, cike da kulawa ta amsa ,dama idan kaga fara,ar ta to tana tare da ya'yan tane . Hajiya Kubrah kenan manyan mata Abubakar ya dubi mahaifiyar sa mum wai yaushe ne su Aleeyu zasu dawo ne sunfa karasa exams dinsu jiyama nayi waya da Usman ba abinda ya tsayar dasu kawai dai shiriritace irin tasu, Hajiya kubrah ta nisa oho sai sun gama hutawa inga zaman London yana musu dadine shiyasa, Amma duk ranarda Alhaji yaganosu kashin su yabushe cewar Abubakar kawai Dan dan sun maida ba a, bakin komai. Ba sun kare exams shine suke tayiwa Abba karya yana tura musu kudi bayan sunsan sun kare Dan kawai rashin kishin kai, kai dakata ra,ayinsune saboda haka ka kyalesu sai ranarda sukaga dama su dawo Kai takura maka akayi dakake karatun, wayene ya matsamaka, baice komaiba dai shi a duniya yana mamakin hali irin na Hajiyarsu kwata2 bata son a takura wa ya'yanta kawai Dan suna da gata Allah dai ya kyauta, To Mum su Afra fa sai yaushe, kaga Malan banason sa,ido towai Ina ruwanka ne kai kake biyan kudin makarantar ne ko ta aljihunka ake biyan kudin meye naka a ciki ,kabarsu suyi abinda sukeso lokacinsune, Umar Faruuq da yaga surutun nasu kara chaja masa kai kawai zasuyi fita yayi daga falon yanufi sashensu Dan Inda sabo yasa ba dajin irin wan nan dramer din ,tsakanin Hajiya da Abubakar, kawai dai shi Abubakar, din ne da na cewa kullun saiyama Hajiya maganar dawowar, k'annensa Nigeria amma amsa dayace take bashi ,shibazai iya hkra yasa masu ido bane, gani yayi idan yabiyewa Hajiya da Abubakar sai sun kara karamishi wani sabon al,amarin gara yabar musu gurin, Dakinsa ya nufa kan bed dinsa ya zube zuciyarsa sai bugawa take runtse idonshi yayi yasake budewa ahankali ya furta I LOVE YOU RUKAYYAH. Sajeeda kuwa yinin ranar a takure tayi shi badadi tasaba komai tare sukeyi ita da sister dinta gashi yau komai ita daya takeyi har break ma kasa yinsa tayi a dadafe taga time din tashi daga skull din yayi koshi , jitake kamar tayi,fira taje gida ta shirya ta tafi asibiti dan ganin Rukayya, Dan batama San an salami Rukayyar ba, haka takeji kamar ma ta wuce asibitin direct. A yauma skull bus dinsu gani take kamar ba tafiya suke yiba Dan bata ganin saurin tafiyar ,yau Sajeeda kenan aminiyar Rukayya, San da mai bus ya ajeyeta da sauri ta fada cikin gidan amma ga mamakinta taga komai tsaf an gyara ko,ina kamshi tashi kawai takeyi ga kamshin girkin mummynsu, bakowa a falon Room dinsu ta shiga ,Ga mmkin ta sai ganin Rukayya tayi akan bed tanata barci abinta hankali kwanace ,wani murmushi Sajeeda tayi najin dadi mai kayartarwa da sauri ta isa , bakin gadon ta Shafa fuskar Rukayya sister ya jikinki hope kinji sauki Dana Rukayya ba. Bacci takeba jin bude kofane yasaka ta kulle ido, bude idonta tayi a hankali ta Dora kanta a saman jikinki sajeeda naji sauki sosai sister I miss u so much me too ,sukayi murmushin jin dadi kamin nan sajeeda ta cire uniform dinta ta fada bathroom domin yin wanka. Maman Ussee😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎2⃣1⃣ Maman Ussee😘 Sajeeda ta fito da ga wanka ta shirya cikin dugowar Riga ta Atamfa simple dinki , dama ita bata Faye yin make up ba inkaga mai Make, up to Rukayyace, Sallar La,asar ta farayi kamin nan ta zauna ita da Rukayya tana gaya mata abubuwan da suka faru yau a skull, ohh kinga har na manta ga book dinki da , aka bani dazu uncle Faruuq ,mtseww Rukayya taja tsaki Sist bar fada min sunansa mugu kawai 😳 cike da mamaki sajeeda ta kalleta wani abune yayi miki hln ,Rukayyah , sai a sannan ne ta tuno da katobarar da tayi but bayanda zatayi dolene ta fadama ,sajeeda gaskya koba komai baxata iya yimata Hidden din komaiba, Nan ne ta sanar da ita duk abinda yafaru . Sajeeda ta dafata kinga kiyi hkr ba shine sanadin shigarki damuwa ba dama dai can su Sister Jameela suna jin haushinki kawai ki rabu dasu Allah yana gani ki rage tsanar da kikayi masa wllhi baki ga yanda yadamu dazu ba danace bakida lfy har tambayana ma yayi a wane hospital, aka kwantar dake nagayamai kinsan kuma ba kyau ka tsani Dan uwanka musulmi Rukayya nasanki da saurin yafewa kiyafe masa kimaida komai ba komai ba zai wuce kinji my Sister, To kawai ta CE amma ga alama maganar bata shiga cikin rantaba tadai basarne Dan bataso Sajeeda ta fahimci wani Abu a cikin zuciyarta ko cewa takeyi hava Dan bakisan azabarda nasha bane shi,isa kikace hakan. Suna zaune a dakin sun dauko sabuwar fira mummy tashigo dakin ta kalli 'ya'yan nata cike da sha,awa tana matukar so tagansu cikin farin ciki da annashuwa, yadai yaran Daddy ana tadine, Rukayya kinsha maganin ki eah tasha mummy yanzun nama ta kare sha ai zan kula da komai insha Allah yauwa yar albarka Allah yayi muku Albarka a tare suka amsa da Ameen. Faruuq kam Sam zaman dakin ya gunduresa jiyake inama ace yasan gidansu Angle da yaje yanxu kozata wulakantashi Amma kuma tayaya shida ba yawo yake cikin garin sosai ba balantana ma ya iya sanin unguwarsu harta, kai ga sanin gidansu Ohh Allah gani gareka , ka sassauta min wani kuna yakeji a cikin zuciyarsa haka ya wuni ba walwalla a tare dashi da kyar yaga marece yayi ya Dan samu yayi wanka yasaka kayan sa Dan yazaga gari ko zai rage zafin ra dadin da yakeji a cikin ransa Dan ya fahimci zamansa shikadai ba karamin kara, dagula masa lisafi yakeyiba. Unguwar mabeera ya nufa gidansu wani friend dinsa yana cikin tukin mota phone dinsa, ya hau ring, kamar karya daga danshi a halin yanxu ba kowane surutu yake iya saurareba indai bana Angel dinsa bane, baima tsaya duba mai kiran ba receive kawai ya lasha ya kara wayar a kunne Hello!!! Daga dayan bangaren aka amsa Hello sweety ykk koba,a fadaba yasan ko wacece Salma kiyi hkr ina driving, ne yanxu zan kiraki anjima. Baima jira cewar ta ba ya katse wayar tare da jinjina hali irin na Salma kullun. Saita kirasa ta wani mayance masa ko anaso dolene oho. Wacece Salma? Salma Kabeer 'yace ga Alhaji kabeeru Mainasara , aminin Alhaji Bashirne mahaifiyar Salma kawar Hajiya kubara CE ta sosai Dan kusan halin su ne yazo daya, shiyasa amintar tasu tahadu saidai ita mahaifiyar Salma tsayayyar mace CE duk abinda tasa agaba to ba shakka saita mallakeshi su hudune a gurin mijin amma saboda kissa da tuggu irin na Hajiya Suwaiba saida tasaka duk aka kori kishiyoyinta yazama ita kadaice a gurin mijin sai abinda tace ta saye shi tamayar da Alhaji kabeeru mijin Hajiya. Su shiddane a gidansu Abdullgafar sai Abdullwahab Da Abdulrahman Sai kuma Salma Da kanwarta Safeeya Salma cikakkiyar yar bariki CE sosai, ta goge sosai da duniya ta hadu da Faruq ne a ranarda sukaje gidansu ita da hajiyarta tun daga ranar da yafara ganinshi taji a duniya batada Wanda takeso sama dashi , duk da tanada nanema duk bata saurarensu tun sanda ta hadu da faruuq da kanta tayi masa talar kanta, butshi ko kallo ma bata isheshiba, Dan shi ya tsani macce marar kamun kawai Wanda Salma na ciki kawai dai yana kulatane sanadiyar Hajiyarsa Dan ya taba yiwa salmar walakanci a gaban Hajiyar ta nuna masa baccin ranta kuma ta umurceshi da karta kuma ganin ya yima Salma walankanci saboda hakan ne yake Dan kulata but har yanxu itace take kiransa da kuma yawan zuwa gidansu acewar ta zo gaida Hajiyar ne kuma ita dama Dan taga Faruuq take zuwa gidan. Faruuq yaja tsaki dama nasan Salmace wllhi baxan daukaba Dan yau najawo kaina kira kenan ba adadi kashe ma wayar zanyi Dan na huta dai2 nan yayi packing a kofar gidansu misbahu abokinsa .wayar ya dauko yakira Misbahun bai wani dadeba ya fito ya shiga motar Faruuq din, suka fice daga unguwar. Maman Ussee😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎2⃣2⃣ Maman Ussee😘 Shigiwar Daddyce ta saka su fitowa domin su gaidasa, ahh lallai Rukayya jiki yayi sauki kina daishan magani ko eah Daddy inasha sosaima to masha Allah,haka aso after sallar Isha kowa ya hallara a falo domin cin abincin dare kamar yanda suka saba ,mummy CE tayi saving dinsu, bayan kowa yaci ya koshi Alhmdllh, suka dawo falo domin yin kallon labarai Wanda kusan ma ince kullun akidar gdn ne kamin time din bacci yayi, saida kowa yara jin bacci San ,nan da guda2 yaran kowa yabar falon mummy kawai aka bari da Daddy ko suma dama jiran yaran kawai sukeyi suma suka kashe duk kayan kallon suka tafi dakunansu domin yin bacci, Sajeeda ta Riga Rukayya tashi daga bacci dayake tasan dawan garin bata tsaya tayar da itaba alwala kawai ta fada toilet ta dauro ta bayar da farali ta dauko qur,ani ta fara karatu cikin muryarta mai dadin saurare Daddy ne ya kwankwasa kofar dakin Amma jin ana karatu ya tabbatar masa da sun tashi daga bacci shima dawowarsa kenan daga masallaci, kira,ar karatun sajeeda ne yatayar da Rukayya da yake a bayyane take karatun addu,ar tashi daga bacci ta fara yi kamin nan tayi mika ta sauko da kafafunta kasa ta nufi bathroom domin yin wanka ta gyara kanta, fitowarta daga wanka daure da towel a jikinta dayan towel din kuma tana tsantsane kanta , dago kai Sajeeda tayi manya masu gari antashi daga bacci eah Sist shine baki tayardani ba to ayi hkr ya jikin naki Rukayya ta kalleta cike da murmushi naji sauki sosai kiyi sauri ki shirya karki makara Allah yabada ladan karatu. Shaf sajeeda ta manta da wai yau ana zuwa skull Dan ganin yar uwarta bata shirya ba a gurguje ta shiga wanka ta fito tafara saka uniform dinta ta dauko sock da sandals dinta yasaka Rukayyace ta daukar mata skull back har suka fito zuwa dakin mummy suka gaidata kamin nan sukaje dakin Daddy shima shirin yakeyi Dan ya ajiyesu ya wuce gurin aiki GT Bank, yadai Rukayyah ya jikin naki Naji saiki sosai Daddy to Allah ya kara sauki suka amsa atare itada Sajeeda, har cikin mota Rukayya ta rakasu Fadil ne agaba Sajeeda da Abdallah kuma a baya ta daga musu hannu har suka bar unguwarsu zuwa skull su Abdallah Daddy yafara saukewa kamin nan ya nufi hanyar skull din su Sajeeda itama ya sauketa direct assembly ground ta nufa bayan gabatarda jawabai aka sallama student kowa yakama Hanyar zuwa class dinsa. A bangaren Faruuq kuma kasa bacci yayi da dare har wani. Zazzabi2 yakeji yana rufeshi da kyar ya iya tashi yasha magani zuciyarsa sai zafi da kunci take masa yakasa controlin din Kansa ,jiyake kamar zuciyarsa Faso kirjinsa zatayi ta fito in bai samu Rukayya ba ,washe garima sanda ya makara tashi Abubakar ne yaji shuru baiga fitowarsa ba ya shiga knocking din door din Umar can cikin bacci yaji ana kwankwasa kofar dakinsa bude idonsa yayi ya kalli agogon dake manne abangon dakin nasa what? Yadan zaro 😳 Ashe har gari ya wayema shut yau na rasa jam,i saboda ke my Angel I love you ya furta a gurguje ya fada toilet ya dauro Alwala ya. Bayar da farali kamin nan ya shiga wanka yana fitowa mai yafara shafawa bayan ya taje Kansa da cum saida ya shirya tsaf cikin shada brown color yasaka hularsa car key dinsa yadauka da Jakarsa ya fito a waje suka Hadu da Abubakar suka gaisa, kamin nan yashiga cikin gida domin ya gaida Hajiyarsa ,Yar mulkin tana zaune a falo da ita. Bacci safe ba akidarta bane bayan ya gaisa da mahaifiyar sa kai tsaye sashen Abbansu yaje yana zaune shima yana karatun alkur,ani sanye da jallabiya ya rusunah ya gaida mahaifinsa , Cike da nuna kulawa Abban Nasa ya karba tare da tambayar Dan nasa ko dakwai wata matsalane no Abba ba komai murmushi Alhaji Basheer yasanya ma dansa Albarka da fatan alkhairi a zuciyarsa kuma yana matukar son Umar Faruuq saboda halayenda na kirki rashin son abin duniya duk da akwai shi a gidansu amma shi kwata2 ba wan nan ne gabansaba, Bayan yagama gaida iyayensa kai tsaye car pack ya nufa yashiga motarsa Dan zuwa skull da kuma fatan ganin sweet Angel RUKAYYAH tasa. Maman Ussee😘 🙎 ' YAR BAIWAH 🙎2⃣3⃣ Maman Ussee😘 Da shigar ,Skull din tarkashensa kawai ya kwasa sai class dinsu yauma kamar kullun. Batanan , sai dai ya kuduri niyar ko tayaya. Ne sai ya ganta Dan bazai iya jure rashin ganin taba fita yayi daga class din Dan dama lesson yazo yiba yadai zo ne yagani kotazo, Bayan break Sajeeda ta fito ta zauna a in da suke zama itada Rukayya daga cikin staff room yana ,hangota sai yayi kamar yasa a kira masa ita kuma sai ya fasa haka ta karashi zaman gurin ta tashi ta koma class ,Dan dama ba dadin zaman ita kadai takeyi ba, After skull hours uncle faruuq bibiyar skull. Bus din su yayi har aka aje sajeeda daga nesa yana hangota ,abin ya bashi mmki matuka gidan Uncle Sadeeq ya furta a bayyanane, dama my angel gidan nan take ,ban saniba , kodai gdnsu kawartane to ai yar uwar tata jiya cemin tayi sister dinta batada lfya it means cewa a gidansu daya najene ko kuma na tsaya, wadan nan sune tambayoyinda yayita yiwa Kansa baisamu mafita ba gashi He can go without seeing her, ya Dade a tsaye a gurin da yayi park daga bisani ya yanke disition zai je gidan bayan sallar jumma,a dayake yau Friday ne, Sajeeda yauma kamar kullun tashiga gdnsu da sallamar ta ba kowa a falo direct room dinsu tashiga Rukayya. Na zaune tana linke kayansu, Sist sannu da dawowa yauwa kema sannu da gida ya jikin hope kinji sauki ,aikuwa gashinan kin gani cewar Rukayya murmushi Sajeeda tayi kamin nan ta shiga cire uniform dinta , mummy CE ta leko dakin nasu yadai Ruky ina sajeeda tashiga wanka yanxu OK to kuyi sauri Dan yau fita zamuyi daku unguwa inaso Ku rakani in an taso sallah , Ku shirya kamin time din yayi , Dama Rukayya zaman gdn ya gundureta Neman wurin fita kawai takeyi ga dama ta samu da ga nan take yiwa Sajeeda magana cewa mummy tace suyi sauri Dan unguwa zasuje basu wani. Bata lokaci ba Dan sunmafi mummy d'okin zuwa unguwar , after masallaci suka fito daga gidan sunsha kyau kam daga su har mummyn tasu rigar shadda CE a jikinsu dinki gown ne ya dibesu sai mayafi dasu kayi rolling dashi mummy kuma less ne a jikinta ta saka babban mayafi da jika, a daidaita suka tare suka shiga bayan sun fada masa Inda zaya kaisu. Faruuq kuma da isarsa gida wanka ya fada bayan ya fito wasu kayan yasaka shadda fara Sol dinkin ta zarce ya amsheshi sosai ya saka hula da agogo turare sa ya dauko ya fesa Magic Dream bayan ya fito daga side dinsa cikin gdnsu ya nufa cike da fara,a yau yasamu solution din matsalarsa, sai dai mi yana shiga cikin gidan Salma ya hango a kan daya daga cikin kujerun falon ta wani hakimce tana taunar cwiengum kan nan nata ba dankwali yasha Karin gashi wasu matsiyata kanya ne a jikinta ko sheda da kyar take iya yinta a zuciyar Umar cewa yake mtseww sai ita gani take ta hadu macce ba kamun kai awa diyar arna jiwani zama datayi don Allah a hankalin yayi sallama Wanda in ba kwantar da hankalinka kayiba bazakaji meyake cewaba Salma ta dago a hankali suka hada ido tayi saurin kashe masa ido daya wow ta fada kayi kyau sosai Faruuq baima bi ta kantaba ya ficewarsa sama ya gaida Hajiyarsa kamin nan ya cemata zaije masallaci. Umar ta kira sunansa idan kadawo I have something to talk about with u so don't be let Tau kawai ya amsa ya fara saukowa daga saman, Yana tafiya a hankula kawai ji yayi an rungumeshi ta gabansa . Saurin fincike ta yayi kamin nan yashiga koramata jawabai ke bakida hankali ne meye hka zaki wani rikeni keba musulma bace hln to bara kiji as from today don't u ever try to do such a thing angain mtseee yaja tsaki ya dingijeta yayi ficewarsa murmushi tayi don't mind Faruuq u will soon be mine and only mine, ta haura sama zuwa dakin Hajiyarsu Umar din. Maman Ussee😘 🙎 YAR BAIWAH 🙎2⃣4⃣ Maman Ussee😘 Da fitarsa. Bai zarce ko,inaba sai mosques bayan an idar da sallah yadade yana addu,a Allah yabashi Rukayya yasaka ita alkhairice a tare dashi bayan ya tofa cike da kwarin gwaiwa ya nufi car dinshi bayan ya tayar da ita bai zarce ko,inaba sai unguwar Arkilla sai dai cikin rashin sa,a gidan a kulle yagashi shin kodai mistake din gida nayi dazu ko kuma idanunane suka hango min gidan da. Bashi bane ohh God wai neyake faruwa dani ne ji yake kamar ya fasa ihu yadade a nan inguwar bansamu wata mafita ba kamar yayi kuka dauriya kawai yakeyi shikadai yasan irin azabar ra dadin da zuciyarsa kemasa ji yake idan bai samu Rukayya ba yana gab da kamuwa da ciwon zuciya ohh love luck what u made me do, jiki a sanyaye ya shiga gidansu kwata2 yama manta da maganar Hajiyarsa , direct room dinsa ya shiga bai wani jimaba phone dinshi yafara ring ya dauka sunan mum. Dinshi yagani daga wayar yayi tare da Sallama daga dayan bangaren tace ya banganka ba koka mantane ohh sorry Hajiya nashigo kainane yake min ciwo but ganin tafe ta katse wayar, a kasalce ya tashi yafito zuwa jin kiran mahaifiyar tasa ba kowa a Falon stairs yafara takawa a hankula kamar kazar da kwai yafashe a ciki da sallamar sa yashiga room dinta saman kapet ya tarad da ita tana cin fruit. Ba kowa a dakin sai ita dayanta air condition aiki kawai yakeyi, Hmmmm Hajiya kubrah kenan manyan matan duniya gaidata yayi cike da kulawa ta amsa shuru yadan gifta na minti 5 kamin nan ta gyara zama ta maida hankalinta a gurin danta Umar faruuq. Sunan sa ta fara kira ya karba ,dama ba komai ne yasaka nayi kiranka ba saidan in shaida maka sakon mahaifinku hakkine a wuyanmu mu fada muku alhamdullah Dan uwanka na yi masa magana yabani confidence sosai kai nakeso naji ta bakin ka aure mahaifinku yakeso kuyi Dan Ku ba yara bane and lokaci daya za,ayi bikinka kaida Abubakar nakirashi yafada min dakwai wadda yakeso to sauran kai inkanada wata wadda kukayi alkawarin aure da ita to saika fada Dan aje anema maka aurenta in kuma babu ni inada zabina saboda haka kai nake saurare, Umar da tunda Hajiya kubra ta fara magana yayi mutuwar tsaye duk da sanyin dakin zufa dai ke karyo masa yama rasa bakin magana tayama za ayi masa maganar aure yanxu bayan wadda yakeso ko sani ma batayiba forget about bata saniba inma tasani iyayenta zasuyi mata aurene yanxu ss one fa take what did she know about aure kai impossible ,iyayenta ko saurarensa ma ba zasuyi ba then what is d solution now , muryar Hajiya CE ta katsesa look Umar mu iyayenka bazamu hango maka abinda zai cutar dakaiba na baka. Nan da kwana biyu ka kawo min matar da zaka aura ko yar waye inbakada ni inada wadda zan gadaku aure tare Salma na fahimci tana tsananin kaunarka Kaine dai kake yi mata wulakanci ,Dan haka na yanke hukunci matsawar baka kawomin surukata ba to ka shirya tarbar Salma a matsayin. Bride dinka ,what? Salma fa kikace Hajiya yes ita Salmar dai dakasani meye bata dashi ba mace bace ko kafitane so go an think before na sake kiranka , Faruuq ya mike idonsa sunyi jajir kamar gauta zuciyarsa kamar ta Faso kirjinsa ta fito yama rasa mezaice da kyar yakai Kansa room dinsa har wani jiri yake gani hava yaza amasa haka bayan yanxu ne yake so yafara budewa Kansa sabuwar Rayuwa shida angel dinsa kamin wani lokaci zazzabi mai zafi ya rufeshi shi da kyar ya iya kiran abokinsa Dr. Khamal Dan ya Duba sa wan nan kenan. A bangaren su Rukayya kuwa tun da suka fita unguwa basu dawo ba sai bayan la,asar sunsha yawo kam Dan sunga gari sosai har kasuwa saida suka shiga mummy tayi sayayyar kayanda take bukata daga nan suka dungumo cikin Adaidata sai gida A falo suka zube Dan dayake daddy yadawo suka gaidasa ohhh shine kuka fita harda patient din idan kuka kwaso mata rana fa gashi yau anyi rana, lah daddy ai taji sauki sosai cewar Sajeeda kedai kunason yawo daine ba wani sauki karfin hali dai gabaki dayansu sukayi dariya Rukayya tace Allah Daddynmu nasamu sauki sosai tau Baby Allah yakaro sauki yabaki lfy mai amfani aka amsa gabaki daya da amin after All Daddy tace sai Ku huta muyi shirin zuwa cikin gari again da murna sukace a shirye muke ai ohhh kajisu sarakan son yawo to da boys dina kawai zani ko my boys suka CE yes Daddy bazamu dasuba tunda mummy da Girls ta fita dazu muma da Daddy zamu fita yanxu ,mummy tace jealousy kukeyi to nima ai sai mun sake fita dasu watarana Daddy ya kashe mata ido daya basai na bari ba murmushi tayi zama ka bari ai duk Kansu kowa dariya yakeyi cike da so da kaunar yan uwansu bayan magrib daddy ya daukeso zuwa yawon shakatawa Dan dama already duk Friday sai sun zaga gari Dan su Debe kewa sunkan sha garin Dan suyi yawo sosai basu suka dawo ba sai 10 :pm kowa da sayayyarsa a hannu dashigarsu gida kowa room dinsa ya fice bayan sun yi sallar insha suka watsa ruwa sai bacci dayake sunci sun koshi asuba tagari Sajeeda& Rukayya 'yan biyu. Mummy da Daddy Maman Ussee😘 I REALY THANKS FOR UR CARE MY FANS LUV U ALL😍 🙎 YAR BAIWAH 🙎 2⃣5⃣ Maman Ussee😘 Washe gari tun da safe su Rukayya suka tashi bayan sun idar da Sallah suka fara gyare gyaren gida koda mummy ta fito har sun kammala da komai dayake yanxu tana barin su su Dora breakfast danshi ba wuya kegareshiba suyan arrish daine sai Dora ruwan zafi sun saka komai a mu halin da ya dace suka koma room dinsu Dan suyi wanka bayan sun gaida mummy da kuma Daddynsu, fitowa sukayi da shirin zuwa islamiya kai tsaye dining area suka nufa basu wani bata lokaci ba suka kammala cin abinci kai tsaye suka fice dakin mummy sallama sukai mata suka fice zuwa islamiya. A bangaren Umar faruuq kam abin yayi worst sosai Dan da kyar ya iya tashi yayi sallar magrib da isha wani zazzafan zazzabi ne ya keji duk da anyi treatment dinsa Amma ji yake kamar baisha komai ba bacci kam a ranar sai dai barawo har abinci kasa cinsa yayi washe gari haka ya tashi jiki ba kwari yadanji sauki dai irin nasa Dan har sallar asuba yaje bayanda gari ya waye yaje cikin gidansu gaida Hajiyarsa ba laifi ta amsa masa batare da wata damuwa ba kana ta CE INA fatar kana nan kana yanke disition din da ya dace dakai ko eah kawai ya bata amsa gud haka yanada kyau breakfast dinma bai wani ci abincin kirkiba yadan tsakura kadan yatashi ficewa yayi daga gidan Dan kwata2 baya jin dadin zama gidan garinma ya isheshi yakusa barin garin gaba dayama ya huta haka ya wuni a ranar ba dadi dayan bangaren zuciyarsa yana mararin ganin RUKAYYAH ga kuma Hajiya ta taso shi gaba. Rukayyah da sajeeda. Basu dawo daga makaranta ba sai 12:pm da zuwansu falo suka zube suna hutawa mummy ta fito daga room dinta sannu da gida mummy yauwa yaran Daddy kuna lfy a makarantar to Alhmdllh suka amsa mata to masha Allah haka akeso bayan sun gama hutawa sukaje dakinsu suka ajiye kayan su sukan Dan kwanta su wuta kamin time din sallah yayi basu farka ba sai 2:pm koshima mummy CE ta tayar dasu Dan karfe ukku zasu koma Islamiya bayan sun idar da sallah abinci sukaci suka sake ficewa zuwa islamiya Dan daukar karatun marece sai 6:pm suka dawo gida a gajiye basu wani dadeba magrib tayi suka fice zuwa dakinsu Dan gabatarda sallah. Haka Rayuwarsu ta kasance har weekend ya kare Monday morning ko waccensu ta shirya tsaf cikin uniform dinta suka dauki skull bags dinsu zuwa makaranta Dakin mummy suka shiga sukayi mata bye bye daddy ya dauke su zuwa skull dasu da su Abdallah da Fadil bayan ya ajiyesu ya ficewarsa zuwa gurin aikinsa bayan an kare Assembly kowace student ta nufi class dinsu do daukar darasi dayake ma text za,a fara musu yau Dan sun kusa fara exams yauma kamar kullun zaune yake cikin staff office ya rasa abinda ke masa dadi abubuwa duk sun cakude masa kwata kwatama ya manta yau yanada Class dinsu Rukayya before break yayi zurfi cikin tunani sai jin murya wata student yayi uncle muna da kaifa yanxu munta jira munji shiru shine mukazo muyi biko dago Kansa yayi OK Fateema ganin zuwa kice su shirya yau text zan muku kinji ta amsa da to yabata sauran kayansa ya CE ta fice masa dasu kamin yazo. Bai wani bata lokaci ba yabi bayanta Rukayya na zaune a sit dinta hankalinta kwance fuskarta daka ganta. Ba wata damuwa a tartare da ita da shigarsa class din ita ya fara tozali da ita baisan lokacin da ya saki wani Kayataccen murmushi ba😇 a zuciyarsa cewa yake Alhamdullah my Angel taji sauki bayan an gama gaida shi shap shap yafara rubuta a saman white bord questions ya rubuta kamin nan yace every body should take a sheet of paper we are going to write, a text yes uncle suka amsa Rukayya batace komai ba Dan ita har yanxu bata huce dashiba duk da Sajeeda ta roketa da tabar komai everything ,yazama normal , bayan ta Rubuta name dinta a paper bata wani. Bata lokaci ba ta fara rubuta text dinta saidai duk dagowar da zatayi sai sun hada 👀 dashi abin har ya soma gundurar da ita shikuma gogan ya kifa mata manyan Idanuwansa ko kiftawa bayayi ciki da so da kulawa wani sabon kaunarta yakeji yana ratsashi duk wani motsinda zatayi yana lura da ita dayaga ta dagoshi sai ya Ciro phone dinsa ya fara latse latse nan kuwa pics ne yake snapping dinta. Batama saniba yayita daukata pictures sunfi a kirga itace first data fara somiting din text dinta ta koma sit dinta ta zauna ita duk ta kagara yan class dinsu sukare text din Dan bama tason zama sa a class din nasu shikuma jiyake kamar suyita zama a haka after an kare text din karbar papers dinsu yayi ya fice daga ajin cike da shauki koba komai dai yau zuciyarsa zata samu sawaba kuma ya dauki pics dinta zasu debe masa kewarta. Maman Ussee😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎2⃣6⃣ Maman Ussee😘 Zaune suke a gurin da suka saba zama domin. Yin break shikuma Faruuq yana cikin staff room yana hango ta sai dariya takeyi da murmushi abin ya matukar kayatar dashi har a cikin zuciyarsa wani sabon farin ciki yakeji yana matukar kaunar Rukayya bayaso yayi missing din ganinta koda na minti dayane haka ya wanzu da kallon ta har suka koma Class Ya Salaam! Ya ambata Wai wace irin soyayyace haka yakasa fada mata and kuma a kullun ji yake soyayyarta na kara ratsa zuciyarsa. Bai wani jima a skull din ba ya fita Dan dama sabida ganinta ne yake daukar time a skull din direct gidansu ya nufa da motarsa da shigarsa cikin gida yar gdn sa ya tarar a Falo tawani hakince kallo daya yayi mata ya dauke Kansa tasowa tayi da niyar yi masa magana hannu ya daga mata ke dakata look Salma na fada miki tun ba yauba nidake bamu daceba and u still don't understand me, plzz ina rokonki 4 d last time let me alone karki hadani da Iyayena Dan indan har kika kuskura kika shigo Rayuwa ta u wll regret, smiling tayi kamin nan tace ai kuwa baka isaba umar Faruuq weather u like it or not u wll marry me am yours,you're my and only me mtseww yaja tsaki it seem like you're not in your sense ,shiyasa kike maganar abinda bama zai ta ba yuyuwa, ai kuwa. Baka Isa ba Dan nice mahaifiyar ka kuma dolene kabi umarnina abinda nikeso shi zakayi yau kwana ukku kenan banji komai daga gareka ba saboda haka na yanke disission and it is Final , saboda haka kawai ka saurari zuwan Amaryarka Salma. Cewar Hajiya Kubrah tunda ta fara magana umar mutuwar tsaye yayi kasa motsa yatsansa yayi ji yayi jiri na Neman ka dashi kasa saurin rumtse idonsa yayi nawasu mintuna yasake budewa jiyake kamar a cikin marfarki Salma yagani zaune akan ciyar Hajiyarsa tana mishi murmushin mu gun ta , dakyar ya iya saita zuciyarsa Dan idan baikai zuciyarsa nesa ba kila a yanda yakeji zai iya kashe salmar kowama ya huta room dinsa yashiga yadade yana tunani kamin nan wani nannauyan bacci yasace shi, Rukayya dabatamasan meyake faruwaba tana zaune Class dinsu hankalinta kwance har aka tashi daga skull suka fice warsu gida itada Sajeeda . Haka Rayuwarsu ta kasance har akayi Holiday tun ranar kuma bata sake ganin faruuq ba duk da tanaso ta daina tunanisa Dan bataga dalilin da yasa take sha,awar ganisaba a yanxu Dan tasan ba shiri sukeyi ba itadashi amma meyasa nake muradin faninsa oho tabaiwa kanta amsa kawai mantawa zanyi dashi Dan ba abinda ke tsakanin ni dashi haka kurun tunanina yarasa Wanda zai tunano sai wanda na tsana bayan anyi musu Hutu bada dadewa ba Daddy ya shirya musu tafiya Raba itada Sajeeda Dan acan zasuyi hutunsu hakan yayiwa Rukayya dadi ba kadanba koba komai zataga mamanta da Baaba dakuma Abbanta kasa boye murnarta tayi har Ranarda suka daga dayake su biyu kadai Zasu Daddy sarkin tsaraba a kullun baya gajiya da lalurori haka ya shirya musu tsaraba mai tarin yawa yatafi dasu domin yakaisu gida murna gurin Baaba kamar me taga jikarta ta kara girma gwanin sha,awa nan nan kawai tayi da ita Daddy kuwa yasha Addu,a kamar me Dan kuwa malan Sa,idu harda kwala yayi gurin iya Daddy godiya bakomai ai yiwa Kaine Rukayya tamkar 'yace a gareni nadauketa tamkar Sajeeda basuda wani banbanci a gurina Salame kam saboda kunya kasa magana tayi saidai murmushi bataso ta zake da yawa saboda Rukayya yar farice a gurin ta ,kwanan Daddy daya ya juya zuwa sokoto Dan aikinsa yakuma gaya musu ranarda zaidawo daukar su ba laifi yasha Tsaraba shima irin tasu ta mutanen k'auye shike da mutunta juna aka Rabu ana murna da farin ciki saidai duk da Zamansu a can din bai hanata tunanisaba har mamakin kanta takeyi lol Ruky an kamu da son uncle F😂😂😜 Sajeeda takanyi mata kirafi akan yawan tunane tunane but sai kawai tace mata bafa tunani komai nakeyiba kawai dai INA kewar mummy da Daddy ne haka zata kyaleta but itama kanta tasan akwai abinda yake damun sister dinta batason fada ne kawai kuma zata kyaleta inayi tsami saji cewar Sajeeda Umar kam tun ranarda yakoma gida yahadu da baccin rai yayi alkawarin barin kasar kozai samu sawaba ga jiya sai shirye _shiryen aure sukeyi Alhaji Basheer kawai take jira aje asaka rana a biyawa diyan ta sadakinsu Dan kam harta hada lefe nagani na fada duk ta zauce ji takeyi kamar ma ace gobene saurin auren Dan kuwa Hajiyarsu Salma asiri taketa banka musu itada danta ganin ko anyi ma Umar baya tasiri shiyasa suka maida kambun yakinsu zuwa ga Hajiyarsa ba laifi a gurin su Dan kwalliya ta biya kudin, sabulu hakonsu na gamda cinma Ruwa. Shikan Faruuq BISA yayi ta zuwa umara Dan acewarsa gara yakaiwa Allah kukansa kozai rage zafin ra dadin da zuciyarsa ke masa bada dadewaba ta fito bai fadawa kowaba sai randa zashi yayi musu sallama ya fice yayansa ya ajiyesa airport jirginsu yadaga sai kasa mai tsarki haka ya wanzu ba dare ba rana yana Addu,ar samun Rukayya Allah yasa ita alkhairi CE agaresa Alhmdllh addu,arsa ta karbu Dan kuwa yanxu Rukayya batada wani aiki saina tunanin sa kwata2 wan nan hutun a Raba bata wani yi enjoying dinsaba. Maman Ussee😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎 5⃣7⃣ ~Maman~ ~Usseey~😘 ★ Masha Allah Abu yayi kyau Domin An Daura aure Lami lafiya komai yatafi yanda yadace Yayinda Yan Daurin Aure suka nufo Hanyar Dawowa Sokoto Dan Can Ne Bidirin Yake Dayake Daurin Auren. Ne kawai Malam Sa'eed yace azo Gida ayi sauran komai Yabarwa Baban Amarya wato Shugaban Biki Daddy😊 Wanda Yayi Alfahari da Hakan,, da Baban Rukayya yamasa. " A bangaren Amarya kuwa tun Safe aketa shagalin Biki Amarya wanka ,, kawai take Dauka na mutunci Ba karya kam Sosai tayi kyau misalin . Karfe Hudu aka Fara walima Wanda Akayi Nasiha mai Ratsa jiki game da zaman Aure da yanda Hakkin miji yake akan matarsa. sosai Abin ya ratsa Jama,a Sai gab da magrib Aka yi Addu,a Allah yabawa Amarya zaman lafeeya da Samun zuri,a Dayyaba ,,Aka watse tun Kare walima Rukayya da Sajeeda keta Kukan Rabuwa Duk Wanda yagansu sai sun Basa tausayi Saida . mummy Ta nuna Baccin Ranta kamin Suka Hakura Dan Dolene su Rabu dama Sabo akewa kuka. ★ Uwargida kam tun da FAROUQ yayi Fushi ya tafi taketa jin Badadi a Ranta,, Haka yaturo mata Sakon cewa Zai turo Ta Dauki abinda Takeso Yau zasu Tare a Sabon Gidansa Komai ya zuba mata aciki kawai Dai ta tattare abinda takeso Dan By 3:pm Zai turo adauketa ,, Tana kare karanta massege din Ta Fara tattara yan komatsan ta Zuciyarta sai Zafi take mata . Haka Yan uwanta da Danginta suka Zauna tare da Ita bamai Bata shawaran Kirki Duk zuga. Ta kawai Akeyi Wanda Hakan kara Ingiza Zuciyarta kawai yakeyi . Maman ta batazo ba Acewarta sai An gama Biki Zata Zo da Sabon Tuggu Dan Tasamu labarin cewa Salma Nada Juna biyu yanxu sun samu Gidin zama . A gidan Umar Farouq . (ohhh kuji min Mata 'yarta fa ke Auren Farouq din Amma ita Dukiyarsa,, CE kawai A Ranta Allah kashiryar Damu kasa mufi K'arfin Zukatan mu Ameen) Haka suka wuni Har Gurin 3 din kamin Yaturo aka Dauki Salma da Sauran K'awayenta Da yan Uwanta yan Kore masu Rakiya . ★ Ba,a Zarce dasu Ko,ina ba Sai Gidan Farouq Dake Unguwar Guiwa lowcost ,,, Gidane Babba nagani Nafada An kawata gidan Ba karya indan Nace Zan Iya Fayyace muku Yanda tsarin Gidan yake Yazama ,, Waist of Time . 😜 Lol . part Biyu ne A gidan sai Garden da Kuma Dan karamin swimming pool ,, da Filn Wasan Ball kusan Irin Ukku Basket Bolly da Kuma Hand Ball. Sai shuke shuke da kuma parking Space . Wanda yake da isowarka ,, Gidan Mutuwar Zaune Salma tayi ta sake Baki tanata Kallon kayyatuwar ,, gidan A Ranta take cewa Ohh All This is myn Wata ,, Zuciya kuma take cewa Ku biyu fah mtseww..... Taja Tsaki Wallahi dai Kishiya batayiba Acid CE Hava ,muna Zaune kalau a Hadani da ,, yar bakin Ciki zaki Ganene inkin Shigo Gidan Wata kawartace tadan bugetah tace . ” ke Ki fito Mana kin wani hakince a Cikin mota ni na matsu naga ,, ya cikin gidan yake Dan gaskiya Salma ur lucky kinga yanda gidan ya Hadu kuwa Sakowa tayi ta Nufi Dayan part din taga A Rubuta kamar Haka “ This Belongs' to RUKAYYAH!!! A Ranta Tace ,,, Ohh Farouq Dan Rainin Hankali ne jifa Ko gidan ban saniba gashi ,, Duk Nama Rasa INA ne Nawa part din Mai gadine ya iso Gun da Take ya ,, Rusuna yace Hajiya ,, Ga makulin Part dinki gaya can Karba tayi bayabo ba Fallasa ta nufi Dayan Part Din sauran Jama,artah suka Rufa mata Baya ,,Ta bude ta Shiga “Ni ma dai Sauri nakeyi na Shiga na ganewa Idona Menene Acikin Gidan Dan gaskiya Ba karya fah ,, Wow„ na Furta A Hankali. Dan A gaskiya ,, Ba,a cewa komai wani Makeken Falone. Na Hango D'auke da Wasu Kayyatattun Kujeru komai Na Falon Black ne da White ,, Kai harma pent din Jikin Bango ,,, Dan Kara min koridor nagani Wanda Zai sadaka da Store da kuma Kitchen daga ka zagaya kuma Ga Dinning nan sai kuma wata yar Hanya ,, Wanda Zata sadaka da can Cikin gidan Dayan bangaren kuma Dakuna ne kusan ,, Guda Hudu a Jere sai Daya kuma A ,, Gefen Wadan nan da Alama Guest Room ne wato D'akin Bak'i . Sai kuma Wata Hanya Daga gefe Can na nufa ,, Wani Katon Falon nagani A gurin ,, Shikuma an masa Kwaliyar Pink komai pink da White color Fantastic na Fada ,, Tare da Zuba Idanuwa na Dan nabasu Abincinsu Shikuma Kofa Biyu ne nagani da Alama Dakin Mai Gidan ne Wata Hanya nabi naga kuma ta sadani da Dinning anan Nan ,, Ne Nafahimci Falon Maigidane Dana Salma Sai aka Sanya Kitchen a Tsakiyarsu dakuma Dinning Area ,, dawowa nayi nashiga Kifarda Naga su Salma sun Bude sun Shiga ,,,Zaune nayi Dana Hango wasu Mayyun Leader sit, Kut🙉 mai kud'i ya More Wan nan Dukiya haka da aka zuba a Gidan nan Kuryan Room din wani Gadone Hadararre mai Rumfa! ★ Suna Tafe ina binsu a Baya ,, Kowane Room sanda muka Shiga ba karya gaskiya Dakin , mai gidane kawai banmu shigaba Dan a kulle yake Falon suka Dawo nima nasamu Gurin zama ,,, sai Kallonsu nikeyi yayinda my Usseey. Yaga Ana shan Juice kala2 yaje yadauko Daya yafara sha banma lura ba sai Ganin shi nayi yanata zukar lemu ,,, Zare Ido nayi nace Kai 🙄 Rufa mana Asiri da shegen kwadayi gobe ma Bazan taho tare dakaiba Dan kar ka k'ara Kwasamin 😂 lol. ★ Yan Daurin Aure sun ,iso lafeeya yayinda Ango da Abokansa basu Zarce ko,Inaba sai sabon Gidan FAROUQ . Dan anan zasuyi liyafarsu . yana isowa Kota kan Salma baibiba kawai Wuce ta yayi ya Shiga Dakin sa,, kawayenta sai tsokanar sa sukeyi suna Ango kasha Kamshi Murmushi kawai yamusu ya fice abinsa Salma ,,ta bisa a Baya yana Shiga itama ta Shigo Zatayi Magana yadakatar da ita da Hannu Durkushewa tayi ,,tafara mai kuka Abinda Bayaso kenan Dole ya Rarrasheta ,, Harsuka shirya kunsandai Mata da Miji sai Allah ,, Haka ta Daure suka Gaggaisa da fans Dinsa yayinda aka Bata kyata kala2 Kawayenta ke karba suna godiya,, yayinda Bakin Farouq yaki Rufuwa Har Gab da magrib kamin suka watse Dan suje akai Ango gurin Wankisa 😀. ★ Shirye2 aka farayi na zuwa wajen Wanke Amarya ,, Wanda ba,a Bata lokaciba ,,, Aka kaita bayan an karene Aka dawo da ita gurin mummy kuzo kuga. Kuka anxo Rokon gafara Haka mummy ma sanda tayi kwallah saboda sabo ,, kakar Amarya sai Baaba sai tsokanar Rukayyah take . haka taje Gurin Daddy dakyar ta Rabu dashi Dan Saida yamata wayo ta Hakura haka suka nufi ,,Gidansu FAROUQ aka damka Amanar Rukayyah a Hannun Hajiyarsa sosai tayaba takuma karba ta sanya Alkhairi Kamin aka wuce da ita Zuwa Gidanta Wato Gidan Ango FAROUQ . " Salma najin tsayuwar motar kawo Amarya Hankalinta ya matukar tashi ,,Jitakeyi wani. Abu na taso mata kamar Zata mutu . haka ta Daure ta Gimtse har aka Shigo da Rukayyah Lullebe da Mayafi ,, Aka Damkata Hannun Uwargida Sarautar mata Dakyar Salma tayi control din kanta Dan,, jinsu kawai takeyi haka suka karaci Surutunsu ,, suka Ja Rukayyah Zuwa part dinta Wanda komai Dayane Dana Salma saidai ita Kalar na Rukayyah Pupplene da White ba laifi Daddy yakashe mata Kunya Dan itama an zuba mata dukiya wane Diyar wani Shahararren mai Kudi ,, Rukayyah Bata taba Tunanin Zata kasance Haka A Rayuwarta. Ba wan nan wata BAIWAH ce daga Allah Da Addu,ah a Bakinta tashiga har kuryan Dakin ta suka ajeta Saman Bed. Yayinda kowa yaba tsarin gidanta yakeyi wasu kuma Cewa sukeyi Rukayyatu tayi dace mudai Fatanmu Allah yabada Zaman . lafeeya da Zuri,ah Mai Albarka. ~Maman~ ~Usseey~😘 “Special Thanks to you my Beloved oneces ,,Bazan taba mantawa dakuba Nagode Sosai da Kwarin Guiwarku a gareni ” ★ Maman Khairy Allah ya Raya mana Ummul-khair.😇 ★ Ummu -Alkhairi B. B😘 ★Bintu Tijjani Zaifada 😍 ★ And my Lovely Aunt Sister Zainab Mai Kano Allah yakawo yan Biyu Ameen😀. Thanks much more Luv u all my Fans Lodi-Lodi😘. 🙎 'YAR BAIWAH 🙎5⃣8⃣ ~Maman~ ~Usseey~😘 ★ Gidan Amarya ya Rage daga Sajeeda sai Afra da Afnan da wasu Fans Dinsu mutun Biyu ne su Biyar kenan. Yayinda Rukayyah ke lullub'e a Mayafi Zuciyarta sai duka takeyi ,, Wai yau itace a gidan Aure gidan Umar Farouq abu kamar Almara . "Sajeeda tace wai yaushe ne Zasu kawo wan nan Angon ne 10:30 fah Afra tace kin San sai anmasa Huduba kuma kinga Sai sun tsaya Dan Kinga dakwai masu so Su yi masa Naseeha Dan Rike macce Biyu sai jarumi Sajeeda tayi Dariya tace Tab kenan . Yayanku Jarumi ne ko Afnan tace sosaima ,, kinga zai nunawa Sistern ki Jarumta irin tasa Aisha tace kai kudaina Tsoratata mana kufa zolayace daku Safeena tace No way Ai dolema ya Hakura saboda Sabon Shiga CE Sajeeda tace Ohhh kukan Allah yashiryaku kunga kamar naji Tsayuwar mota may be gasu nan sunzo Suka kara feshe ko,ina da Turare kamin suka sami Gu suka zauna Rukayya Hawayene kawai ke zuba a Idan nuwanta Dan yanxu ne yakara tsinkewa lol😜. ★ Bayan an kare wankin Ango Gidansu aka nufa Dan Ayi masa,, Hudu ba sosai Alhaji Basheer ya Masa Nasiha mai Shiga jiki yayi Adalci a Tsakanin su karya nuna musu banbanci Kuma ya Rike su Amana,, Ya tsaya tsakani da Allah karya fifita wata akan wata ya kwatanta Adalci . Haka aka kaisa gurin Hajiyarsa Itama dai Fadan tamasa na a Rike Aman da Adalci ,, daga nan aka Daukeshi zuwa gidansa Abokansa sai tsokanar sa sukeyi ,, Shikuma sai Dariya kawai yakeyi yana Wani jin Dadi har suka iso Part din Salma suka nufa dashi ,, Suna Zaune itada Kawayenta daketa zugata da Sallama suka ,, Shigo aka tsaya Akayi jawabin na Salma ta zauna lfy da yar uwarta Kuma Farouq ya kwatanta Adalci ,, Akayi Addu,a Kamin aka Baiwa Salma Kayanta na tande tande ,, Ba yabo ba fallasa tayi masa saida Safe shima ya mata ya lura sosai Bata cikin Kwanciyar Hankali,, amma bayanda ya iya haka Suka Ja Farouq zuwa part din Gimbiya Amarya . ★ Da Sallama suka Shiga yayinda wani Daddad'an kamshi mai sanyaya zuciya ya doki Hancinsu da Sanyi mai Dadi ya Ratsa su har Kuryan Daki inda Rukayyah take suka kai Farouq sai Daukan su Photo akeyi gwanin kyau Haka aka yi Barkwanci da Haka dai suka karasa komai suka D'auki Su Sajeeda Domin kaisu gida ya Rage daga FAROUQ sai RUKAYYAH . What a wonderful Day Shurune ya Ratsa Nadan wani Lokaci Yayinda Farouq yayi gyaran murya yamatso kusa Da Rukayyah ya Bude mayafinya tare dacewa . Amincin Allah ya Tabbata gareki yake ma,abuciyar Kyau. Girgiza mata Kai yayi Dan Ganin Hawaye ,, a Fuskarta Hannu ya sanya yashiga goge mata Fuskarta yayinda ya umurceta data tashi ta Dauro Alwala su nunawa Allah Farin Cikin su Da Zuwan Wan nan Ranar mai Albarka. " Ba musu tashiga toilet tayi Alwala shima yashiga yayi yajasu jam,in Sallah Raka,a Biyu sukayi kamin ya matso kusa da ita ya Dora . Hannunsa akanta yashiga yi mata Addu,ah da kuma Fatan Samun Zuri,a Tagari . kamin ya je ya Dauko Plate da cup ya dauko Leda Wata gasaasar kaza yazuba a plate din ya Dauko fresh milk ya zuba dakyar ya lallab'a ta ta ci kadan bada yawa ba kamin tayi brush Shikuma ya fita anan ne Rukayyah ta samu ta zauna a saman bed duk sai taji wani iri saboda Bata saba ba . farouq kam Dakinsa dake part din Rukayya yanufa yashiga Toilet ya washa Ruwa kamin yafito ya feshe Jikinsa Da Turare Yana katewa ya nufi Room D'in Rukayyah Zaune ya tarar da ita Yace a,a wai Ke Zama ma kikayi ,sunkuyar da kanta tayi kasa ya matso kusa da ita yace kinga kidai kije ki cire wan nan kayan ko na cire miki su da kaina Rasa mezatace masa tayi sai murza yan yatsun ta takeyi matso wa yayi kusa da ita ya ,, Fara Rike mata Hannu wani Shock ne taji yajata Dakyar ya lallabata tayarda tacire kayanta ya Dauko mata wata Sleeping Dress .Purple colour. Had'ararriya ta Hadufa ba karya gaskiya yaja Hannunta suka fara zagayawa sanda yanuna mata komai dakomai hard Room dinsa saida yakaita ita dai Takasa sakewa Bayan yakare nuna mata komai ya dawo da ita zuwa Room Dinta Upp din. Wuta yayi yakara A,c suka kwanta Yajawota ya Rungumeta can cikin Jikinsa Jikinta ne yafara Rawa Dayaga Haka sai ya Rada mata a kunne just be Free ba Abinda zan. Maki duk da Haka Bata Sake ba Haka yashiga wasa da ita son Ransa Sanda yakusa Wuce gona da iri Rukayya ta Fara masa kuka badan yasoba ya barta A haka sukayi Bacci Wanda zankira da An daiyi maganin Ace Ba,ayi ba Dan Ba Wanda yayi Baccin kirki acikinsu Sai guraren Asuba ya barta yatashi Dan zuwa masallaci ita kuma ta Shiga Toilet wanka tafara yi kamin tayi Sallah ta zauna tafara karatun Al-Qur,ani Mai Girma har gari ya waye. ★Tun ficewarsu Farouq Salma takasa Zaune takasa tsaye da kyar ta iya control din kanta ledarma ko Kallon ta batayiba fuu tashige Room Dinta kawayentane sukaci kazar Banda kukah ba abinda Salma keyi ba irin Zugarda Zuciyarta batayi mata ba O my God yanxu Farouq dina na can tare da wata ko wane karatun yake koya mata oho Ashe haka mata sukeji idan An masu Kishiya da gaskene Ashe Ba,a Bacci haka ta wanxu cikin Tunani Matar tasiri Har Garin Allah ya waye yanda taga Rana haka taga dare . Shigowar Farouq ne ya sanyata ta fara Baccin karya kamar gaske tayar da ita yayi yace taje ,, tayi Sallah Lokaci yayi kamin yashafa cikinta yabata kiss ya wuce mtsewww taja Tsaki Aikin Banxa Bayan ka gama Lalacewa da wata shine zakazo kamin Dadin baki( Hattara mata wallahi muji Tsoron Allah yakamata musan irin abinda zamu gayawa mazajenmu saboda mumuke Neman Aljannah a gunsu Allah yasa mudace Ameen.) Haka ta Daure taje tayi Alwala tayi Sallah ta Shiga wanka bayan ta idar da Sallah tafito tashirya cikin wata Atamfah Dinkin mai kyau tana ta wani cika da batsewa kamar wadda Akayi wa laifin Wani Abin. " Bayan ya dawo daga masallaci part din Rukayyah ya Nufa ya tarar da ita tana ta karatu murmushi ya sakar mata kamin ita kuma ta Gaidasa ya Amsa ,, yace Yauwa Sarkin tsoro murmushi tayi cike da kunya kamin ta gama ta fito tadan gyara wasu abubuwan Dayake ma komai Normal yake sabo ne kawai dayi Sai Farouq kam Room dinsa ya nufa ya koma Bacci Rukayya ko rasa abinyi tayi taje kawai ta kunnah T.v tashiga Kallo Abinta. " misalin 8:30Am Afra tashigo gidan D'auke da Kayan Breakfast nasu Da murna Rukayya ta tareta tace sai yanxu Afra tace tab koyanxuma sakone,, yakawo ni kinga Ficewata ma zanyi Dan Banaso Yaya ya Yiman surutu yafara cewa INA masa ,,Sakko tun da safe a gidansa ,, Murmushi tayi ta karbi kayan ta jera a dinning table Afra Bata wani jima ba tafice tace Zata dawo zuwa anjima Rukayyah cigaba tayi da kallonta sai gurin 9. farouq ya fito D'auke da Fara,arsa yasha wankan Boyel milk colour ,, yace yadai my Angel ,, tace lfy Lou Kinci Abinci ne ta girgiza masa kai yace A,a Ba tun dazu aka Aiko Da Abincin ba tace eah INA Jirankane yace OK to zo muje muci tare suka ci Abinci saida Farouq ya Tabatar taci ta koshi kamin ya barta Ta gyara gurin ,, ya umurceta data Dauko mayafinta suje part din Salma ,, Ba musu ta yi yanda yace yayinda yake Gaba tana biye dashi Baya har suka is a Part din Zaune suka tarar da ita Da. Sallama suka Shiga Rukayyah ta gaidata Wanda dakyar ta Amsa Farouq ne yanuna mata guri ta Zauna Shuru ne yadan Gifta kamin FAROUQ yafara magana kamar haka : ★ Salma Kinga ga Rukayyah nan Amanace a gurinah kuma a gurin ki Banason Fada,, Kuma Ku zauna lfy da juna Ku mutun ta junanku duk kanku INA sonku shiyasa na zauna tare Daku Rukayyah Ki Baiwa Salma Girman ta karki Rainata kibita Duk abinda takeso indai bamai wahala bane kimata kinsan Junah biyu gareta sai kinyi Hakuri da ita kinji Tace Insha Allah yace Good . Allah yayi maku Albarka yabani Ikon yin Adalci a Tsakaninku Rukayyah tace Amin kamin ya fice ita ma takoma part dinta Dayake Yan Yinin Amarya sun Fara Isowa haka dai Suka kasance Har Rana tayi. Maman Usseey😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎5⃣9⃣ ~Maman~ ~Usseey~😘 ★ Gab da Azhr Su Sajeeda sukazo sosai Rukayyah taji Dadi suka Zauna sukayi ta tadi sai barkwanci sukeyi gwanin sha,awah sai tsokanar ta sukeyi badai ta kulasu banda murmushi ba,abinda take musu Haka suka zauna sai Dare Suka gyara mata Part dinta tsaf sai Kanshi ko,ina yake yi Basuda matsalar Abinci Dan Daga gidan Hajiya Ake kawo musu ,, Koyanxu Abincin aka kawo su Afra suka Ni Driver Dan Ya ajiyesu gida harda Sajeeda sanda suka ajiyeta a gida suka wuce Warsu gida. "Rukayyah wani wanka ta Dauka mai Daukar Hankali ta Zauna a sitting Room tana Kallo Abinta Dan Yau bakonta yazo Hankalinta a kwance. Batada wata damuwa phone dinta ne yayi Ring ta Dauka tare da Sallama ,, mummy takirata da wayar Sajeeda tace Yadai 'Yata lafeeya Lou kike ko tayi murmushi tace lfy mummy ba komai yauwa Dama dan na gaya mikine Ki Duba Acikin Jakar da Sajeeda ta kawo miki zakiga ,, Wasu ledar guda biyu Dayar turarene na Humrah a Ciki dayar kuma maganine ki sha da Madara tace tau Insha Allah sun tan taba Hira daga Bisani Kuma suka katse wayar . ta sauke Ajiyar zuciya kamin ta ci gaba da Kallon ta. ★ Farouq Bai dawo gidan ba sai guraren 9:30pm Da shigowarsa bangaren Salma ya nufa Baiganta anan fallo ba ya Shiga Dakin ta kwance yarar da ita Hawaye duk ya Bata mata Fuskarta ,, wurin Gadon ya nufa Ya kira Sunan ta Salma. Bata kallesa ba Tace wai Salma menene yake damunki Kwanan nan duk Kin wani Rame kin Hana kanki sukuni wai menene Nifa ban kara Aure Dan na muzguna mikiba Dan Allah ki cire komai Aranki please hava Kamar wani abu duk kinbi kin Hana kanki sukuni Batadai ce dashi komaiba ya Rugumeta yafara lallashinta ,, dakyar yasamu ta Hakura shiya bata Abinci da kansa ya bata maganinta tasha Dan yaji Jikinta yayi Zafi saida yaga tadan Fara Bacci ,, kamin yatashi ya wuce bangaren Rukayyah . ★ Da sallama yashiga wow" Ya Furta a Hankali saboda wani Daddadan kamshi da Sanyaya zuciya Daya doki Hancinsa Amsa Sallamar sa tayi tare da Gaidasa ya Amsa yace hope dai Bakiyi Fushiba Dan na makara tace No Bakomai Yace OK Kinci Abinci ta girgiza kai yadan Bude idonsa yace tomeyasa Kosai tare dani Batadaice komai ba ta saddan kanta ,, Kasa tana murza yan yatsun ta Matsowa yayi ya Shafa Gefen Fuskarta Yace zan Cire wan nan kunyar Dan. Naga Alama Zata takurani yanufi Room Dinsa saida ya Rage kayan Jikinsa ya yasanya Short Nikkah da Yar Singlet ya fito Kallo Daya tamasa Ta sauke kanta Kasa ,, Hannunta ya Ja suka nufi Dining Dan Cin Abinci Sunayi suna Yar Soyayya Nakuma gefe Inata Kallon Ikon Allah. " Bayan sun Kammalah kowannensu Dakinsa ya nufa Rukayyah Brush tayi ta watsa Ruwa ta sanya Nightes masu shegen kyau Jajaye ,, ta Bude Tuearenda Mummy ta Aiko mata tashafe Jikinta dashi ko,INA Kamin Ta zauna kusa da Bed Dinta tana Kallon pictures din da Sukayi Dazu itadasu Sajeeda. Farouq ne yashigo Dakin Shima Kayan Jikinsa Ja ne masu Guntun Hannu Zaunawa yayi kusa Da ita Yace mugani ta basa wayar sukaci gaba Da Kallonsu tare Wani yayi Dariya wani kuma yace kai Kukam dai Kun iya Daukan photo to bari nayi mana wani pic din ,, Ya Jata sosai ajikinsa yamasu photo Selpic Kamin ya Dora mata kiss Wanda ya Ba,in kashe mata Jiki ,, Turning Off din Wutar Dakin yayi yafara Yimata wasan ni Da Zafi Zafi Wanda Rukayyah ta Kasa Gane Ko tantace a ina take ,, Ganin Zai wuce Gona da iri yasanya ta CE dashi Bakonta yazo ,, Dakyar ya iya Control din Kansa Amma fah Duk da Haka ,, Tasha Wahala Dan Dakyar Ta lallabasa ya Hakura ,, Amma yadan samu Relief sosai Rugumeta yayi sukaci gaba da Bacci Kulle musu kofa nayi Tare dayimusu Fatan tashi Lafeeya. ★ Sajeeda CE kwance a Room D'insu sai juye juye take saboda tasaba komai tare sukeyi itada Rukayya yaigashi Bata jin motsin kowa Lallai Yaune take jin Rabuwarsu da Rukayyah Dan Abin duk yataru yamata yawa gara Jiya Dakwai mutane to Yau kowa yayi Tafiyarsa Abin ba Dadi A Hankali ta Furta tace I miss You Sister. Allah yabaki zaman lafeeya da Kwanciyar Hankali. Wayarta ta Dauka tashiga whatapp ,,, Dan ta tagewa kanta lokaci da Dare . saida tafara Jin Bacci ta Ajiye wayar Ta kwanta Sai Safe Daddy ya Buga mata kofa ta Tashi tayi Sallah tadanyi Karatun Al-,Qur,ani Sai Karfe 8 Tatashi tashi Kitchen Dan Ta Dora Breakfast ,, A kitchen Mummy ta Tarar da Ita Tace Hoo sannu Yau kinyi Abin kanki Murmushi Sajeeda tayi tace Mummy an tashi lfy tace Lou Yau kin fito Da wuri tace eah Mummy tace Dan kinsan Ba maiyine keda kikeda Son jiki Murmushi Sajeeda tayi kamin suka ci Gaba da Hada komai a Tare Har suka kammala Hada komai Suka jera a Dining ,, Kowa yakoma Dakinsa Sai 10:Am Suka fito sukaci Abinci kamar yanda Suka Saba Kullun ,, Daddy yace Allah Sarki 'Rukayyahtu ana can mummy tace Ashe Bamu kadai ke Missing dinta ba yace gaskiya Baku kadai bane ,, Yauwa Sajeeda Gobe Ki shirya kifara zuwa skull Ki shirya da wurifa Dan nasan Halinki tace Angama insha Allah yace Good ,, suka ci gaba da cin Abinci bayan sun kare Sajeeda tashiga gyara gurin mummy kuwa Tashiga kitchen Dan Ta Dora Girkin Rana . ★ Da Asuba Farouq yatashi yayinda ya gyarawa Rukayyah Kwanciyar ta Dan Jiya baibarta tayi wani Baccin kirkiba wanka yafara yi ya nufi masallaci Dan Gabatar da Sallah sanda yanufi Part din Salma ya tayar da ita kamar Yanda yayi jiya ,, Bai shigo. Ba sai Da aka kare Sallah Yadawo Room dinsa yanufa ya kwanta. " Rukayyah kam bata Tashiga sai ,,, Guraren 7:30Am toilet tanufa tafara wanka tayi Brush kamin tafito tashirya tsaf da ita daganinta kaga Amarya yauma kamar jiya gyara ko,ina tayi ta fesa Turare tadawo Ta zauna tana Kallo a Sunnah T.v Kwankwasa kofa taji anayi ta tashi ta Dauko mayafin ta kamin ta bude kofar Driver ne shikadai D'auke da Breakfast yace gashi inji Hajiya tace a Gaidaki Rukayyah ta karba ,, Tace yauwa kace Angode Nima ina gaidata ta Kulle kofar ta jera komai a dinning ta ci gaba da Kallon ta Hankali kwance . ~Maman~ ~Usseey~😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎6⃣0⃣ Maman Usseey😘 ★ Sai guraren 10:Am Umar Farouq yatashi sai wanka yafara yi Kamin ya shirya tsaf Ya fito ya tarar fa Rukayyah nata Kallo da murmushinsa ya iso gareta tare da Shafa Fuskarta,,, Amarya Bakya laifi ko kin kashe Dan masu gida . tadanyi fari da Ido tace Bama zan kashe kowa ba Yace to muje muci Abinci Dan Nasan Bakici kina jirana ko kai kawai ta Daga masa yaja Hannunta suka nufi Dinning area. " A tare suka ci Abinci Yana ta tsokanarta bayan sun karene yayi ficewarsa ita kuma tashiga gyara gun dasuka bata Ta wanke Kayanda aka saka musu ,, Abinci a Ciki ta sanyasu cikin basket Dan dama Haka takeyi idan An kawo Na Rana sai ta Bayarda na Safe hakama idan an kawo nadare saita Bayarda . kayan Rana Da Safe sai ta Bayarda na Daren Tadawo ta Zauna ta Rasa Abin yi kawai sai ta kira Abbanta bayan sun gaisa yake Tambaya ta ya Sabon guri Tace lfy Lou Alhamdullah ,, Haka sukata fira yabaiwa Ummanta harda Baaba ma sanda suka gaisa Daga nan Ta katse wayar ta kira Daddy shima Tambayarta yayi ya sabon wuri tace Lfy Lou ya kara yimata Nasiha mai Ratsa zuciya game da Zaman Aure ya Sanya mata Albarka haka tayi ta kiran Yan Uwa da Abokan Arziki Suka gaisa Harsu Afra saida ta kira Tace su Turo mata No din Hajiya bayan Ta kammala wayar ne Ta kirata cike da girmama,, Daga dayan Bangaren aka Amsata sosai Hakan yayiwa Hajiya Dadi ta Tambayeta dafatar Ba Wata matsala tace Bakomai lafeeya Lou yauwa Haka akeso Allah yayi maku Albarka Rukayyah ta Karba da Ameen ta Ajiye wayar Ta Dan kishin gida kadan Batasan Sanda Bacci ya kashe ta ba . ★ Farouq ne Zaune a room Din Salma wadda yakasa Gane ma kanta cikin kwanan nan Yana dai Biyematane Dan Bayaso Yashiga Hakkin Ta Allah yagani Bazai iya jure Rainin Hankali ba Dakyar yasamu ya lallasata taci Abinci saikace Gareta Aka fara Kishiya duk ta fita Hayyacinta Bayan taci sosai ya Bata magani Tasha Shida Kansa ya mata wanka yadawo da ita ,, Room dinta Ya kwantar Kamin ya yi Ficewarsa Dan Amsa kiran da Alhajinsa kemasa. " Haka Rayuwarsu Takasance a Tsawon Satin nan Har Ranarda Ya Raba masu Girki Ya Kara tarasu Ya Musu Nasiha mai Ratsa jiki Wanda Rukayyah kawai ta Dauka Salma kam Biris tayi Dan Ita yanxu Kwata2 ta canja daga Sanin da Farouq yamata Salma ce Zata Fara yin Girki Wanda Farouq ya CE Duk mai yin Girki to A part Dinta Za,aci Abinci Hakan bakaramin Haushi yayiwa Salma ba Amma ba yanda ta iya Dole ta Hakura Dan tasan Halin FAROUQ Baya canja,, maganar sa " Shikuma yayi Hakan ne Dan A kara Samun Had'in kai A tsakanin su ,, " Da Dare Salma ta Rangada Girki Mai Rai da motsi yayinda ta Ci uban make ,,upp kamar ba itaba ajima Anjima ,,ta Duba agogo haka Ta tsara komai sai wani Kisisina takeyi Farouq baidawo ba sai misalin 9 Bangaren Salma ya nufa Da murna ta Taresa Shikuma sai wani Biye mata yakeyi Dan Farouq Mutun ne maison a tarairayesa nan da nan ta Gama dashi Room dinsa suka Nufa ya Rage kayan Jikinsa . Ganin Abin na Salma bamai karewa bane yasa ya dakatar da ita yace Dear sorry kinsan yanxu Bamu kadai bane Jeki ki kira kanwarki muci Abinci Kinga tana Jiranmu badan Taso ba ta Tashi yayinda Shikuma yadawo sitting Room yana jiran Isowar su. ★ Rukayyah na Zaune A Dakinta Bayan ta karasa Sallah Isha Dan yau tayi Wanka karatun Al-Qur,ani mai Girma takeyi Da murya mai Dadi a gurin mai Saurare Salma tashiga Noking din Door Rukayyah bataji ba Dan Dayake karatun ya D'auke mata Hankali Abin ya matukar Tunxura Salma tace Lallaima wan nan Yarinyar dani take Zance murda kofar tayi tajita a Bude Sa kai ,, kawai tayi Mutuwar tsaye tayi Dan Yau itace Rana ta Farko data taba shigowa part din Rukayyah tun Kawota A cikin Zuciyarta tace Tab Wan nan Dukiya da aka zuba mata a gidan nan kamar wata yar Hamshakin mai Kudi A Hankali ta fara Notice din komai Har kitchen sanda tashiga bata Tsinkeba saida Tashiga Room din da take jiyo Saurin Kira,a natashi bako Sallama ta Bude tashiga Zare Ido Tayi dataga Wani Hadararen Royal Bed ,, Da kyar ta Hadiye Yawo Tare da gyaran Murya Rukayya bata Dago ba saida takai Aya ta dago da Murmushi a Fuskarta Lah Aunty Salma kece yau Shigo Zauna mana Yake Salma tayi tace No bazama Zanyi Abinci zaki fito muje muci Rukayyah tace OK ganinan zuwa Barin Room din Salma tayi Tana ta Magana a cikin Ranta lallai wan nan saina Tashi Tsaye yarinya kamar yar Tsana Hmmm Tabdi ,, tayi wucewarta zuwa nata part din Nidai Binta nayi Da Ido INA Kallon Ikon Allah 😀. " Rukayyah Kara Feshe Jikinta tayi da Turare Aoud mai Dan Karen Kanshi kamin ta Dauki mayafinta ta Rufe Jikinta tana tafiyarta Hankali kwance Harta Isa Part Din Salma da Sallama tashiga ,, Part din Fuskarta D'auke da Murmushi Farouq ya Amsa shima murmushin yakeyi Gaidasa tayi tamin ta samu guri tazauna Batare da Bata lokaci Farouq yace muje muci Abincin ko Salma sai Hararan Rukayyah take Ganin irin Kallon da Farouq yake mata A Ranta tace Jarababa yaudai kya kwana ke kadai mayyah kawai( Jama,ah kujimin Salma Da Wani zance oh oh mata Da kishi ) Rukayyah batamasan tanayiba Samun Kujera tayi yazauna Abinta yayinda Salma ta fara zubawa kowa Abinci Tanayi tana Jan Hankalin FAROUQ Wanda Gabaki Daya ya Mutu a gurin Kallon Rukayyah Dakyar yasamu yayi control din Kansa ya kula Salma Bayan sun Kammala cin Abinci suka Dan Taba Hira Sama2 Rukayyah tayi musu Sallama Zata wuce Farouq yace Angel kona Rakaki ne Tace no Kayi zaman ka Badamuwa Salma tace wane irin karakata Halan dazata zo wanine ya Rako ta , no kinsan Yanxu Dare yakara yi kar taji Tsoro Turo baki Salma tayi Yace lallai nida naje kiranta Dazu wani ne ya Rakani Ganin Zata miyarda Zancen wani Abu yasa ya Dauko wata Caftar aka Basar da Zancen. ★ Sosai Salma tayi mamakin Ganin Irin yanda Farouq yaketa Rawar jiki Daya ,, kusanceta Kwata2 Batama yi Tunanin Samun irin Haka daga Garesa ba Baccima Kalilan yayisa Wanda Hakan ba karamin Dadi yayiwa Salma ba a Ranta tace wayasani koya Canye abinsa kamin a shigo karyar Banxa Anxo ana mana wani fankama ashema nafita sai Rawar jiki yakeyi akaina ina Amaryar Haka tata kitsawa Har Bacci ya kwasheta . Rukayyah Baiwar Allah Tun da tadawo part dinta tarasa Abinda kemata Dadi Saboda a kwanan nan tasaba sosai da FAROUQ yaugashi Zata kwanta ita Daya wata Zuciyar kecemata yanxu yana can Yana yiwa matarsa irin yanda yake maki wani Abune taji yataso mata Ganin Tunanin ta zaiyi yawa shaidan zaiyi tasiri akanta yasa Tace "A,uzubillahi minal shaidanirrajim" Ta Basar da Zancen kwanta wa tayi a beda dinta sai juye juye takeyi Ganin Rakasa Bacci yasanya ta Dauro Alwalah tashiga yin Nafillah Sallar dare Dan Neman Samun Zaman lafeeya da Kwanciyar Hankali Yauwa maccen Kwarai Diyar Albarka Saliha acikin mata nagaidaki Macce Tagari. Maman Usseey😘 🙎 'YAR BAIWAH 🙎6⃣1⃣ *Maman* *Usseey*😘 ★Washe Tun da Asuba Farouq yatashi Yata yar da Salma Kamin ya Fito ya Nufi Part Din Rukayyah Dayake yanada keys na kowane part . Bude Kofa yayi Yashiga a Hankali yake jiyo Sautin Muryan ta Tanata Karatun Cikin Murya mai Dadin Saurare Murmushi Yayi Yace Alhamdullah a Fili Wani Dadi ne ya Ziyarci Zuciyarsa ,, Saboda Tun Aurensa Da Salma baita ba Ganin ta Dauko Qur-ani ta Karanta Ba duk da Yana iya Bakin k'okarinsa Wurin Ganin tasamu Ilmi saidai Yau Yakasance Abu mafi Girma a Rayuwar sa Ana Karatun Qur-ani A gidansa Bayan shi Sabanin Wakokin da yasabaji A gurin Salma wata Soyayyar Rukayyah CE takara Shiga Zuciyarsa ,, Sosai da Sosai Da Sallama yashiga Room Dinta Zaune yaganta a Saman Sallaya Sanda takai Aya kamin ta Dago ta Amsa Sallamarsa Da Murmushi ta Gaidasa ,,Barka da Asuba ya Amsa Da Yauwa Hope kin tashi Lafeeya ,, Qlau Alhamdullah , yauwa Nixanje Massalaci dama Dan Natashe kine na manta Matar Tawa Malamace Abin Dariya yabata Tace wane Ni Daliba Dai yace koma Dai menene Allah ya karba ta Amsa Da Ameen Kamin ya Fito Dan Zuwa Massalaci ya sallaci Asuba. ★ A bakin Kofa sukaci karo da Salma wadda tayi labe tana Saurarensu Turo baki tayi Farouq yace Salma Ba Sallah nace Kije kiyi ba To ai gani nayi Ba ita keda Girki ba Amma kawani Zo Part Dinta Nifa Banaso A Shiga Hakkina ,, Hava Salma wan nan Wace irin Maganace Dukkan Ku Magana ne kuma ko wacce tanada Hakki akaina Dan Nazo naga Ya tashi Kuma Natayar Da Ita tayi Sallah shine Shiga Hakki Eah Shiga Hakkine mana Aida Kace Ni naje Na tasheta bakaiba Mtseww yaja Tsaki to Badani a Wan nan Tsarin. Ba Kuma dole kibi yanda Na tsara Gidana yayi ficewarsa yabarta saida ta Harari Kofar Part din Rukayyah kamin ta wuce nikuma nace A Banxa Harara A Duhu Dan Wadda kikayi Domin ita bata ma San Kinayi ba . " Rukayyah bayan ta Kare Sallah Asuba Wanka tashiga tayi ta zauna ta tsara kwalliya kamin tadawo parlour ta Zauna ta kunnah T.v tanata Kallo Abinta wayarta CE tayi Kara ta Duba Sunan My Sist tagani Murmushi tayi tace Sajeeda early in d morning ko lafeeya Daukar wayar tayi Daga Dayan Bangaren Sajeeda tace Amarya Bakya laifi Ya Amarci Rukayya ta Amsa lafeeya Lou gashinan munayi good Dama Yau zan Fara Zuwa Skull Na shirya ne saina tunoki nace Bara nakira naji ki Rukayyah tace Ayya Sist Allah yabada zaman Lafeeya yasa A dace kinga Kallo ma nakeyi Amma Dai zaki biyo tanan ko Sajeeda tace Ban maki Alkawari ba But saidai nagani sun Dan Taba Hira daga Bisani suka Ajiye . wayar " Bayan yadawo daga masjid Yatarar da Salma Sai wani Cika take tana Batsewa a Dole Bai mata Adalci ba Ko kula ta Baiyiba yashi gewarsa Room Dinsa Harda Sa key Alamar Karma ta Damesa Gama Borin Haukan ta tayi tashiga kitchen Dan Hada Breakfast Ita wallahi wan nan Aikin yamata yawa Dole ma yasama mata yar Aiki Dan Bazai yuyu tarika tashi Kullun tana Hada Break ba Gashi ita bama Wani Abin kirki takeci Ba ta Tuna Ada in bataso ba Saidai suyi Baccin su Har su gaji in sun tashi zai Je ya yo musu ,, Take Away Amma yanxu Tun ba,aje ko,inba Tafara Tashin Safe Kai Wallahi Bazata Sabu ba wai Bindiga A Ruwa Wan nan Tsarin Sam Baiyi ba A Gaskiya Kishiya Takura ce Ina Zama na kawai a hadani Da Wahala , wahala mana Gashi duk nagaji Mtseee gaskiya da Sake Ita kadai taketa Sambatun ta kuma dole ta Hada Break din Amma Kamin a kammala Anyi Dogon Baki yafi a kirga tsaki ba, Bayan ta Jere komai A Dinning table kamin tashiga wanka tana Cikin shirya wa Wayarta tayi Ring ,, Ta Dauko. Farouq ne Baima jira maixata ce ba ya CE da Ita idan kin gama Hada Break kije ki kira Yar Uwarki Ya kashe Wayarsa Bin wayar tayi Da Kallo kamin daga Bisani ta Fito Kamar karta je but Sanin Halin Umar yasa taje Dole ta kirata Koda ta Dawo Yana Zaune a Fallo yana jiran su ,, Samun Guri tayi ta Zauna Kamin Da Sallama Rukayyah tashigo Fallon Salma na Lura da Irin Shu,umin Kallon da Umar Farouq yake mata A Zuciyarta tace A Banxa Saboda Kyauwun Fuskar kawai ne Dani ake Tutiya Dariya Tabanifa Sosai ,, na CE Hodi Jan Kishi Gamai Yinka ,, Haka suka zauna A Dinning Salma tayi Serve Dinsu ,, Sanda suka karene Salma Tace Dear ,, Please maganar Yar Aikin nan gaskiya Aikin yamin yawa kuma kaga yanxu Banikai nikeba ga Babynka Banaso Yasha wahala sosai ,, OK. Za,a kawo Insha Allah Dama Mun kammala Zancen Da Hajiya But Ba ke kadaiba Harda Rukayyah ma Hava Dear kasan Mai Aiki Daya fah Bazata iya Aikin gidan nan kawai kamo mata wata gaskiya ,, Rukayya tace No Aunty Bama sai ya samo wata Ba Ai zan iya kawai dai Akawo miki Dan Kar Babyn mu yasha Wahala Murmushi FAROUQ yayi yace a,a Angel kema za,a Sama miki Dan Kema Banaso ki Wahala kinji Wata uwar Harara Salma ta Banka wa Rukayyah a Ranta Tace Nikuma so kake nawahala ba Aikin Banxa,, A,a Dear taya mutun Yace Bayason Abu za,a mai Dole kawai ka kyaleta ba tace Zata iya ,, FAROUQ yace ai Nine nace Zan damo Saboda haka zan Samo muku Ku Duka OK . Badan Taso ba tayi Shuru Dan kar tajawo wa kanta wata Maganar , ★ Haka suka Kansance Har Girkin Salma ya Kare Rukayyah ta Karba ,, Wani Lafiya yan Girki ta Rangada mai Rai da motsi Dayake Rukayyah Rainon Mummy ce Ba wasa gurin Iya Girki Bayan ta Hada komai a Dinning table tashiga wanka tsaf da ita Yanda FAROUQ yasaba shigowa yauma Haka Yashiga Wani Kamshin Dadi ne Ya Ziyarci Zuciyarsa Sannu da Zuwa tamasa kamin ya Amsa da yauwa Room Dinsa ya Nufa bayan yafito ya umurceta dataje ta Kira Salma suci Abinci ba musu taje Ta kirata Saidai Abinda Salmar ta mata Bataji Dadi Ba Tadai Hadiye Saboda Tana mata Uzuri Ne Sai Dan kawai ta Shigo Room Dinta ta kiranta Shine ta Rufeta da masifa Haka ,, aka koya maki In kinga kinyi Sallama ba,a Amsaba kijira mana kawai kiwani shigo min Daki Kamar Kin Shiga kasuwa Hakuri ta Bata kamin yadawo Sanda ta Banna musu time kamin ta Zo da Farouq yamata Magana Cewa tayi Hava wai Meyasa baka Tausayina ne Rukayyah tace Gaskiya Yakama ka Rika mata Uzuri kasanfa yanayin Da take Ciki saida Haka,, Baisake cewa komai ba Har Rukayya tagama Saka ma Kowa Abinci A Zuciyar Salma cewa Take Jiwani Jagwal gwalo Bari dai naci kar Kuma nayi Laifi ,, Dan Ba wuya nayi yanxun nan. " Haba kuzo kuga cin Abinci Su Salma harda Neman Kari😂 Kuma fah Jagwal gwalo ne Haka ta Bude Ciki ta kwashi Girki Sosai ,, Sanda taci Sosai harda Gyatsa ,, lol😜 Dear Please karakani Zuwa Cikin Gida Dan gaskiya na koshi dayawa fa Kai Salma Sai kace A wurinki aka Fara yin Ciki da Murmushi Rukayyah tace Hava Dai Raka ta Din da zakayi shine wani Abu please Rakata mana ,, Dole ya Rakata Amma Daya Biye mata Allah kadai yasan abinda Za,ayi Sanda yakai Zuciyarsa nesa kamin Ya samu tabarsa Hmmm macce Shu,umar Gaske ce . ★Bayan yadawo ne Ya tar da Rukayyah Harta Gyara komai da komai Sannu da Aiki yace da Ita cike dajin kunya Murmushi tayi ,,masa kamin suka Dan Zauna a Fallon sunda n taba Kallo nawani Lokaci Daga Bisani Farouq ya Dauketa Zuwa Bed room Dinsa Yace Kallon ya isa Haka gobe kya Karasa ko ,, murmushi kawai ta Sakar masa Kamin ya bata Hot kiss Toilet yashiga Hakan ne yabata Damar Zuwa nata Room din ,, Ta canja nata Kayan Tana Cikin fesa Turare taji Murda kofa Bata Duba ba Dan tasan Mai Shigowar Ji kawai tayi An Rugumeta ta Baya tare da Cewa shine kika Gudo ko Toni na kawo kaina karban Turaren yayi ya Ajiye a Saman Mirror ,, ya Juyo da ita Suna jin Nufa shin Juna dago Fuskarta yayi Batayi Auneba taji Bakinsa a Nata Ba ko ,, Sassautawa yashiga Tsotsar Lips dinta Wani Yanayine marar Fassarawa Rukayya ta Tsinci Kanta Ciki ,, Ganin tsayi ya Gagaresu ,, Yasa suka Zube a saman Bed Sai wani Shafa ta yakeyi ta ko,ina Tuni Farouq ya fita Hayyacinsa Dakyar ya iya tashi Ya kashe wutar Dakin Da Zafi Zafi FAROUQ yake so ya Isar da Sakon ninsa yayinda Rukayyah najin Salo yafara Chanjawa ta Rokonsa Dayiyi Hakuri Amma INA Baimasan tanayiba Saboda yariga yayi Nisa Acikin Wata sabuwar Duniyar da Ya Tsinci Kansa Ganin Labarin Yagagari Saurarena Yasa nabarsu suji Dadin Shakatawa Nima Naje na Rugumi Nawa Ogon 😀 Maman Usseey😘 Note: A Duniya mutane kala2 ne wasu masu Hankali ,, Wasu kuma Allah Dai ya Kyau ta Magana itace Yakamata makiyana sugane cewa Zakaranda Allah yanufa da Chara sai yayi saboda Haka Duk mai Zagi yakama Jikinsa ,, Saboda zagi Baya qari kuma Duk Wanda Ya Zagi tsohon wani Nashi ya Raina Ni mai Hankalice so Bazan Biyewa mai zaginah Abinda kawai Nasani Ko Cikin mutun na Ciyo Bazan Daina Rubuta yar BAIWAH ba Idan kinji Zafi Gobe ki Rubuta naki Kuma bansaki Karatu Doleba so Kiyi Hakuri Nagaba yayi gaba nabaya sai Biyar Sahu kuyi Hkri Hater Bayanda Zakuyi Dani. Masoya nah nagode da kulawanku Maman Usseey love you All😍 🙎 'YAR BAIWAH 🙎6⃣4⃣ ~Maman~ ~Usseey~😘 ★ Kwanci Tashi Lokaci K'ara Wucewa kawai Yakeyi Yayinda Komai Sake Canjawa kawai yakeyi Amma Sha,anin Gidan Umar Farouq kam Abin Ba,a Cewa komai Tun Ranarda Cikin Salma ya Zube Shikenan Suka Kasa Hakuri Ala Dole wai Dasa Hannun Rukayyah Dan Ganin Irin Kulawanda Yake Baiwa Salma Shine yasaka mata Magani a Abinci Cikin ta Ya Zube Allah Sarki Salma takasa Ganewa Abin Daga Allah ne Saboda likita ya Tabarta Da Cewa Ba wani Abinda yayi Course Din Problem Din Kawai Dai lokaci ne Da kuma irin yanayin Mahaifar ita Salma din. Sosai Farouq yaji Bakin Cikin Zubewar Cikin Salma sai Dai Ba yanda Ya iya Saboda Allah ne Mai Bayarwa Wata kil Hakan Shine Alkhairi A garesa Yayinda Salma da Mahaifiyar ta Kuwa suka Lashi takobin Sai sun Sanya Rukayyah Kuka Kamar yanda Salma Tayi sun Dauki Laifin da Batajiba Bata Ganiba Sun Daura Mata . " Haka Rayuwar su tayita kasancewa Kullun Kudinsu na Hanyar Malamai da Bokayen Yan Tsibbu Sai Dai Har yanxu Sun kasa Samun Nasara Saboda Rukayyah Mutun CE mai Riko da Addini Bata wasav ko kadan Yayinda Hakama Farouq ko sunyi Abin Baya Tasiri Maimakon su Saduda Kara kaimi ma sukayi wurin Ganin Sun Cimma Burinsu. ★ Rukayyah na Kitchen tana Hada Girki Dan Yau Ita keda Aiki yayinda suna Makale a Waya itada F Dinta Sai Kyalkyalar Dariya takeyi Da Alama Zancen yana mata Dadi ,,gaskiya My F Yau karka Dade Dan Banason A kalle min kai A Hanya kamin Kadawo Gida ,, daga Dayan Bangaren yace Aikuwa Kamar kinsan Yau Saina Dade Dan Kuwa Tadi Zani Yau Turo Baki Tayi Hadi da Buga Kafa irin Wanda Yara Sukeyi Please Nidai Kadaina Min Irin Wan nan wasa Allah basonta Nakeyi ba kwai kwayonta yayi Tare da Yin Murmushi Karki Damu My Angel Ur D Only One ai Daga ke An. Rufe kofa Kinji Zan dawo Very Soon Insha Allah ,, Fadada Fara,anta Tayi Kamin taci Gaba da Hada Girkin ta mai Rai Da Motsi Tanayi tana Duba lokaci Duk da Tasan koya Dawo Ba yanxu zai Shigo ba Sai anjima Amma Dai Tafiso Yadawo Da Wuri ,, Haka ta Kammala komai Da Komai Ta Jera a Saman Dinning yayinda taje taci Wanka Tasanya Kaya Masu Bala,in Daukar Hankali ,, Ta Zauna A Sitting Room Tana Jiran Isowar Farouq Dinta . ★ Farouq kuwa Baidawo ba Sai Bayan Isha Dayake Yanxu Ba Tare Suke cin Abinci da Salma ba Ganin Bataso Yasanya ya Umarci Kowa Da Yayi Nasa koba Ranar Girkin Mutun Ba ,, part Din Salma yanufa Dan Dama A ka,idarsa Duk Wadda tafita Girki Sashenta zai Fara zuwa Kamin ya Je gurin Mai Girki Da Sallama ya Shiga Cikin Gidan Tana Zaune Tana Danna wayarta Bako ta Amsa masa Baiyi Mamakin Rashin Tarbonsa Dabatayi ba Dan Dama Ya lura Kamar kar ya kara Aure ta Canja masa More Especially tun da Rukayyah Ta Daina Shigowa Part dinta wata Rana Haka Zata Garashi Sai Sunyi Nisa ta Janye Jikinta Ala Dole sai sunyi Jinga Shida Matarsa Amma Bayanda ya Iya Saboda Bayaso yashiga Hakkinta ,, Kuma yana Kyaleta ne Dan Kawai kar Ace Dan yayi Aure ne Yake mata Wulakanci Wuceta yayi ya Shiga Dakinsa Ya Dauki Abinda Zai Bukata Kamin ya Fito ya Ya Ajiye mata Ledar ta Yace Sai da Safe Bako Godiya Balantana tamasa Magana Harara kawai Tabisa da ita yana Fita taja Wani Dogon Tsaki Mtseeeww Zaku Sani ne daga Kai Har Waccan Shegiyar Rukayyar Ta tashi Ta kulle Part din ta Tayi Shigewarta ta Kwanta Saka Banxa Saka Wofi Har Barawo yasaceta Bacci. ★ Cike da Haushin Salma Farouq ya Fito yanufi Part din Rukayyah A yaune yaso Yabasu Gift din Motocin da Ya Saya Musu Tun da Dadewa Amma Baccin Ran da Salma ta Sanya mishi yaji Yama Fasa Kyautar ,, Wai meyasa Mata Kishi yamusu yawane yatuna irin Rayuwar su DA sukayi a Baya Ya Ce Allah ya Kyauta ya Shiga part din Rukkayah Yana Bude kofa wani Daddan Kamshi yamasa Maraba Lale ,, Tana jin Bode kofa ta gudu tazo ta yi Hugging dinsa Ta Shiga yimasa Welcome Back Kiss Tare da Yimasa Sannu Dazuwa ,, Neman Damuwarsa Yayi ya Rasa Jansa tayi sai Room Dinsa Bayan ta Ajiye kayanda yashigo dasu Hada masa Ruwan wanka tayi Tare da jansa zuwa toilet cikin Wani Salo mai Rikitar da Mai Tunani Cikin kashe Murya tace My F kayi wanka Sai kaci Abinci kona Tayakane murmushi yasakar mata Tare da Yawota Ya Rugumeta sosai ya lalubo Bakinta Yashiga tsotsa Ganin A Cikin Toilet suke kuma Tasan Halin Kayanta yasa tadanzare Jikinta cikin Salon Dabara Tace kayi Wanka Dai First Ta kallesa ta Ciremai Kayan da Zai Saka nashan Iska masu kyau kamin taje ta Sanya kayanda Ya siyo a Cikin Frige Wanka yayi Kamin ya Fito Daure da Towel Murmushi yayi a Cikin Zuciyarsa yace Allah yamaki Albarka My Angel Ya Fito ya Gyara Kansa Yasanya kayanda Ta Ajiye masa kamin Ya Fito Zuwa Sitting Room. ★ Yana Bude Kofa Tana Shigowa Kashe Mata Ido Daya yayi tace Wow kayi Kyau shine Baka Jira Nazo na Shirya ka ba,ko Sorry Ai koyanxu Kinyi K'okari Muje naci Abinci Dan Wallahi yunwa nakeji Shafa cikinsa tayi tace Sorry Dear please kadaina Zama da Yunwa Banaso Yace to Ai Yanxu gaki zaki kula Dani sukayi Dariya Chak yadauketa Bai Direta a ko,inaba sai Saman Kujera shima yazauna Ta sanya masa Abinci Amaimakon Taci tana a,a Bashi Tashiga yi Farouq ko Yabude Ciki Sai kwasar Girki yakeyi Sosai yaci Abinci Sanda ya koshi kamin Itama ya Fara Bata Abincin sai Shagwaba take Zuba masa Bayan sun koshi ta Tattara kayan Ta miyar a Kitchen Ta dawo ta kwanta a Saman Jikinsa tana wasa da Sajeen Fuskarsa yana Kallon News Ajima yakan Dan Kalleta yana Shafa mata sumar Gashinta Daya kwanta luf Bada Jimawa ba Bacci yafara yin Awon gaba da Rukayyah Gyara mata Kwanciyar ta yayi Sanda yagama Kallon News Dinsa ya Dauketa Chak bude Ido tayi yace Sarkin Raki Badai Bacci Zakiyi ba Bayan kinsan Ban Baki Sakonnina ba Murmushi tamasa Tare dacewa My F nagaji please bari Gobe Dan Allah Girgiza mata kai yayi tare da Makale kafada. Alamar Naki wayon Bai Direta ko,ina ba Sai Saman Bed Dinsa kamin Ya dawo ya kashe Kayan Kallon ya Rufe ko,ina Yadawo ya Samu Rukayyah Shafa Fuskarta yayi ta Bude Ido Wai My F dagaske Bazaka Hakura Sai Gobe ba Bai barta ta Karasa Zancen ba Yashiga Sance Mata Riga Wasa yafara yi da Duniyar Fulaninta Daga nan Kuma yadawo Yasha lips dinta sanda ya tsotse su Tas kamin Kuma ya Fara Aika mata da Sakonninsa Masu wuyar Fassarawa Da Zafi Zafi Yake Aika Isar mata Sakonsa lol😋😜 ~Maman~ ~Usseey~😘 ta kicin da baranda. Amma komai ni nakeyi. Bana k'in yi mata aiki,saidai idan ina aikin kallo daya zakayimin ka gane rashin sabo. Nan da nan nake gajiya. Abun kona ran bai wuce tarewar dasu Nura da Usman da kuma matansu,Bilkisu da Meena sukeyi ba. Kodayaushe suna nan suna kallo da hira tare dasu Hamida da Raliya tamkar zasu fasa falon. Ni ce zanyita zirga zirgar kaiwa da komowa wajen kawo musu abinci da abin sha. Bilkisu ce mai yaro daya,Junaid. Ya zamana ni na zama yar raino matukar tana sashen. Cire mishi pampers,goyashi,bashi ceralac da sauran ayyuka masu cimin rai. Ga wannan shegen kallon dana tsana a wajen Usman,duk sadda muka hada ido sai ya hau yimin murmushi yana kashemin ido,harararsa nakeyi alokacin saidai wai an tsikari kakkausa ko a jikinsa. Hindatu kadai ke tausayamin. Bana kwanciya bacci saina kammala ayyukana. Abu daya naki yarda da gyarawa,dakin kwananmu,rantsuwa na yiwa Raliya a gabanta akan cewar bazan gyara ba tunda nikam shimfidata,Kafet ne. Sune masu kwanan gadon,bandaki kuma duk sadda zanyi amfani dashi zan gyara idan ta kama. Zata mareni naja baya nace wallahi ta mareni saina gayawa Abba. Nasan ba tsorata tayi ba,saidai bansan dalilinta nayin kwafa ta fice ta kyaleni ba. Hamida tayi wuf ta taso zatamin fitsara,ta juyo ta daka mata tsawa. Wai ita saita mareni din taga abunda zanyi,ganin uwarta ta hanata nayi murmushi nace "Kinci sa'a domin wallahi sai kin gane kurenki muddin kika tab'a jikina." Jin haka ta harzuka ta daga hannu zata mareni,Raliya ta daka mata tsawa,ni kuwa na rike hannun na murdeshi ta fasa k'ara. Raliya ta iso ta hankadani ta janye Hamida sukayi gaba. Na rasa dalilinta nak'in daukar mataki akan hakan,saidai gaba mai tsanani ta shiga tsakanina da Hamida babu maganar dake had'ani da ita. Ranar da zamuyi Graduation kuwa,ban nemi komai daga Abba ba hakanan ban gayyaci kowa daga bangarena ba. Yaya abdullah kadai na shaidawa ta waya, duk da har lokacin baisan Mamma bata gidan ba. Ya tayani murna yace inama yana nan dashi za'ayi. Yayimin alkawarin tahomin da kyauta ta musamman idan zaizo. Murmushi kawai nayi. Sauran kudadena na hada na biya komai da makaranta ta bukata. Ranar kuwa da sassafe na shirya,Hamida sunsan da maganar saidai basu cewa kowa uffan ba,hindatu ma ta shirya cikin uniform kamar yanda dokar makarantar tace dalibanta suyi a ranar. Ta dubeni"Zaki rigamu tafiya ko Tasleem?" Murmushi nayi mata na amsa da eh. Daga haka na dauki yar karamar handbag dana zuba kayan amfanina na fito sanye da rigar T-shirt na school da jeans na gida. Mukayi arba da Raliya,ta daure fuska "Ke kuma ina zaki? Kodayake wannan ba matsalata bace bazan hanaki yawon banzanki,aikina fa? Wa zaiyimin? Kada ki sake kibar gidan nan batare da kinyisu ba." Daga haka tayi dakinta,tsaki naja bana tsoron dukanta balle na Hamza,yau ranata ce babu wanda ya isa ya hanani zuwa makaranta. Ina waige waigen neman direba naji hon,ina dubawa naga Usman zaune a motarsa yana dagomin hannu yana murmushi. "Dan iska." Na fada a fili na kauda kaina..... 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (32) Kai tsaye wajen Baba Maigadi na nufa. Na tambayeshi ko direba yazo saidai ya sanar dani cewar matarsa ke nakuda yaje kaita asibiti ba lallai ne ya dawo nan kusa ba. Bakin ciki ya turnukeni,da ace na iya mota da duk hakan bata faru ba,gashi kuma koda yazo dole ne sai na amso mishi mukulli wajen Raliya domin shaf ina manta cewar mukullayen motar gidan a hannunta yake. Daidai nan Usman ya iso acikin motarsa,baba Maigadi ya tafi don budemishi gate. "Zaki makara fa my sister,zo ki hau na saukeki." Kamar nace bazan hau ba,saidai tunawa da nayi Abba kansa baya gari ballantana nasa ran dakewa zuciyata na amso kudin mota yasa banyi musu ba na shiga don kuwa bani da ko ficika. Ai daman kudin ubanmu ne suke takama dashi,babu laifi don alokacin Abba dayake am shanyeshi a rubutu ya k'ara bude musu shaguna kowanne da nashi a kantin kwari suna d'an maida hankali. Na shiga gidan gaba na zauna fuska a daure. Bai damu Usman ba ko kadan,sai bayan mun soma tafiya naji yace"Ba gaisuwa ko?" Ni wallahi mamaki ma yake bani har lokacin ganin yanda yake yimim sanyi sanyi a yanzu. Banda niyyar gaisheshi,na dauke kaina ma. Yayi dariya"Ke kam don kinsan kin hadu shiyasa kike yiwa mutane yanga Tasleem. Hakane dalilin dayasa kike wulakanta masu zuwa gidan nan da sunan sunzo zance wajenki ko?" Na watsa mishi harara,ko a jikinsa na kauda kaina bance uffan ba. "Tasleem kina da kyau sosai kamar mominki ko ince kinma fita. Gashi Allah Yayi maki baiwar diri ko ta ina ke macece. Dole ki dunga yiwa maza yanga." Na dauki surutan Usman a matsayin wofi,banko kara dubansa. Har muka iso yana zazzaga shirmensa don shirme na dauki zantukansa. Na soma hango take takensa,akwai abunda yake nufi a kaina saidai ko kusa ban nuna alamar na fahimci komai ba. Muna isowa na yunkura zan bude kofar ya dakatar dani ta hanyar cewa na tsaya. Na dakata,kudi ya mikomin har dubu uku ba musu na karb'e ai kudin na ubana ne. Ko godiya banyi ba na fice. Anan muka shirya,sannan muka nufi inda ake taron,Afficent. Waje ya cika makil da iyayen yara da sauran yan makaranta. Tausayin kaina ya kamani sanin cewa bani da wanda zaizo mini cikin yan uwana gashi ko abun rabo banyiba. Haka na kutsa na zauna,saidai a ranar nayi hotuna da kawayena,Munnira da Jamila, da yan ajinmu maza da mata. Saida akayi kirana domin amsar certificate na mike a nutse naje. Nayi mamakin ganin wanda ban taba zato ba yazo da niyyar daukata a hoto. Yaya Musty(dominka,yaya mustyna..love u forever..miss you:ur bloodsis..rufaida) ne,d'an gidan Gwaggo Hafsatu yayar Mamma dake Kazaure. Na saki fuska sosai,ina karba na nufeshi bakina a washe "Yaya mustyna kai dawa kuke tafe? Ya akayi kukasan da wannan ranar?" Ya harareni "Bayan da kika k'i kiranmu a waya ki sanar damu sai Abdullah dake a wata k'asar ne zai gayamana?" Nayi dariya a shagwabance nace "Afuwan yayana,yanzu kai da waye kuke tafe?" Yana dariya yaja hannuna yana fadin "Muje ki ganewa idonki." Haka mukayita kutsawa taron jama'a bai tsaidani gaban kowa ba sai Mamma da gwaggo Hajara. Ihun murna na saki ban damu da wadanda suka kalloni ba. Na rukunkume Mamma kafin na saketa na rungumi Gwaggo Hajara. Bansan ya akayi ba kawai sai na fashe da kuka sosai,har wani malamin Chemistry dinmu sarkin shishshigi ya matso wai bai taba ganin kukan Headgirl ba(kasancewar mukamin dana rike kenan a makaranta)sai a yau. Su mamma sukayi dariya,nikam na harareshi dariya kawai yayi ya kara gaba bayan yace"Madam,your daughter is one of my best students,very talented." Mamma murmushi tayi kawai. Kirana da aka karayi ne naje nayi speech a matsayina na headgirl na mike na tashi bayan na damkawa Mamma certificate dina. Tiryan tiryan nayi na gama na yiwa manyan bak'i fatan komawa gida lafiya sannan na bada shawara ga juniors dinmu nan aka hau tafi raf raf akarshe na koma gasu Mamma mukayi ta daukar hotuna. Munnira da Jamila suma suka iso suka gaida Mamma. Ina zaune kawai sai naga yaya musty ya shigo da kwalaye,nayi mamakin ganin jakunkunan rabo dauke da memo fa handfan a ciki. Na kalleshi idona taf da kwalla,yace "Zaki soma kuma dai? Muddin kikayi kuka zan fasa baki." Gwaggo Hajara tayi dariya "Wannan hukunci yayi." Nayi azamar share fuskata "Kaga nabar kuka yayana." Mukayi dariya,ashe tun sadda na sanarwa Yaya abdullah ya gayamusu. Shine Mamma ta bayar ayimin memo,anan shima Malam ya k'ara mata kud'i. Don farin ciki na rasa inda zansa raina. "Hamida,hindatu." Hamida ta kalleta ta tabe baki tayi gaba,hindatu ce ta tako ta gaishesu. Mamma ta dafa kanta tana murmushi bayan sun amsa. "Ina maminku? Ku gaisheta." Kusan lokaci daya muka dubi Mamma nida gwaggo Hajara,gwaggo Hajara harararta tayi. Nikam mamakin rashin zuciya irin na Mamma nakeyi,bata fushi. Da hindatu kadai na dauki hotuna,a karshe yaya musty ya amshi camera dita da zummar zaisa a wankemin hotunan harda na tasa wayar. Naji dadi sosai. Har kusan azahar muna tare kafin a watse suma su soma shirin komawa Kazaure. Anan ne idona ya raina fata,gwaggo Hajara ta dafani "Haba 'yata,menene abun kukan? Kiyi hakuri,tunda kunyi hutu saiki tambayi Abbanki idan ya amince sai kizo mana koda sati kiyi kinji? Kukanki sai ya karyar da zuciyoyinmu." Suka lallabani suka tafi. A ranar kuwa nasha zagi wajen Raliya dana koma,saidai batayi gigin taba lafiyata ba. Aikin da acewarta na gudarwa,dole na yishi. A banza kam tunda na samu ranar nan ta tafimin cikin matsanancin farin ciki. Ban kwanta ba sai wajen goman dare. Anan ma banyi baccin ba don hira nayi tayi da hindatu akan makarantarmu kafin bacci ya suremu........! Tun daga wannan ranar kuma sai na soma sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi hakanan nakan je dukkan wani aiken da zaiyimin zuwa gidansa ko kicin din Raliya da sauransu. Ban dai sakarmishi sosai ba,amma babu wannan rainin sosai. Har kuwa zuwa lokacin bai rabu da fita yawon dare ba. Nasha ganin Meena tazo wajen Raliya tana bala'i akan ita ta soma gajiya da bin mata irin na Usman,mutum tamkar wanda aka yiwa asiri. Raliya saidai ta bata hakuri don babu laifi iyayen meena akwai naira hakanan takan lasawa Raliya sosai domin ita din macece wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin da ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma business da takeyi,hakan bai hanata hangen na wasu ba. Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya musty yana yimin albishir cewar an daurawa Mammana aure da wani almajirin Malam. Har tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren alhalin ubansu na raye, kai koda ace baya raye akwai yaran dake taya ubansu kishi amma nikam baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma sai na fashe da kuka. Ina cewa shine ko a gayamin nazo da wuri? Dariya yayi yace kada na damu anan Kazaure Mamma zata zauna duk sanda naga dama na tambayi Abba ya barni toh nazo na ganta. Naji dadi kwarai ya kara tambayata game da Yaya abdullah nace mishi sauran mishi watanni uku kawai ya dawo. Daga haka mukayi sallama tare da alkawarin idan yaje gidan zai kirani mu gaisa da Mamma. Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na hau bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki dana ji muryar Mamma a sanyaye har na tambayeta ko bata farinciki da auren nan? Bata bani amsa ba ta share da tambayar lafiyata. Nace alhamdulillah,tace zan cigaba da karatune? Na tabe baki "Bansani ba Mamma." "Kamar ya baki sani ba Tasleem? Keda mahaifinki? Kije kiyi mishi magana tun lokaci bai kure maki ba." Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na gwammace nayita zama haka a gidan. Haka mukayi sallama da ita. Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman ta haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace. Murna a wajen yan gidan ba'a magana. Nikam ko ajikina daman ba wani mutuncinsu nake gani ba. ******* Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na Raliya ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna falon suna kallon wasan Hausa saidai ko inda suke bana kalla ballantana film din da suke kallo ya dauki hankalina don tun fil'azal fina finan hausa ba burgeni sukeyi ba barni da da kallon Indian series da Korea anan kam ko makiyina ke kallo zan saci kallo. Sallamar Usman ta katsesu,Hamid bai amsa ba saima ya mike ya fice saboda a yanzu haushinsa yakeji akaina. Bayan su hamida sun gaisheshi ya dubi Raliya. "Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena ne?" Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko damu ba ta kyabe baki "A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan kuwa batason aikinta ga waccan tsiyar saiku kwasa." Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa ba. Murmushi yayi ya dubi Raliya "A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga gwaggon meena zata dunga yi musu wanka sai Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan." Raliya bata musa ba domin duk yanda zan kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace "Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa ta gama wanka sannan zaki dawo." Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata ta kammala aikin na mike na shiga daki. Haka na tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba da ita ta tuntsire da dariya gami da yimin gwalo"Haka zaki k'are." Kamar nace mata wani abu saidai na fasa nayi gaba,Raliya har lokacin tana falon banko kalleta ba nayi gaba abina a fusace. Saida nazo daidai garden na zube anan na fashe da kuka,wai haka rayuwata zata k'are? Wane irin uba gareni da bai daukeni komai ba? Ya manta da ya haifeni ne har ya banzatar dani a gidansa ya maidani wofi? Ace yan aiki ma sun fini daraja da kima a gidannan? Na daga kaina nakai duba da d'an lilon da muka saba wasa da Yayana. Haka zaiyita cillani yana goyani muna zagaye garden dinnan muna dariya. Ba zato naji an dafani ta baya,nayi azamar juyowa ganin Usman bansan lokacin da naja tsaki ba nayi kokarin mikewa yayi saurin dawowa ta gabana. "Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna kina kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki bayan ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi." Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban kyauta ba,nace "Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma me na tsarewa mutane ba." Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo hannu zai dora kan lebbana nayi azamar ja da baya,cikin tsoron yanayin kallon da yakemin "Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi. Ni bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa dani shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika kware a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA ce, banason ganin gidan nan da kazanta. Don Allah kanwata wallahi tana yin arba'in I promise you zaki komo gida." Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi gaba yana magana ko juyowa banyi,menene saukin da nan da can din? **** Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief) dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da niyyar share hawayen. Ta dubi Haris wanda shima ya gaji da waigenta ya karkato gaba daya yana duban fuskarta don jin dadin hirar. "Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman komai na rayuwata ya soma tabarbarewa. Yanda akayi kuwa shine......." 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (33) Kwana uku da yin candy dinmu,Abba ya dawo daga tafiya hakanan Hamid shima ya dawo daga makaranta anyi musu hutu. Zuciya irin tawa ta hanani tunkarar Abba da zancen zuwa Kazaure. Sai ince rabona da sanya Abba a ido tun sadda yayi kirana yayimin batun komawa sashen Raliya da zama. Wataranar asabar ina gugar falon Raliya,ina yi ina wake wakena wanda yana daya daga cikin abunda ke konawa Raliya rai ganin bana nuna damuwa a dukkan ayyukan da take sanyani. Saidai batasan cewar kawai dannewa nakeyi amma ji nakeyi kamar na shak'ota don bakin ciki. Hamid ne ya shigo da takalmi ya bi ta inda na taka zuwa bakin firij,na kalli yanda wajen ya b'aci da k'asa bance komai ba na k'ara gogewa,yazo ya kara wuce hannunsa rike da lemon b'awo yana sha yana yarda kwallayen nan ma bance uffan ba don na lura tsokanar fad'a yakeyi. Saida nazo daf da kammalawa ya kara tahowa zai shige. Ai kuwa na sanya mop din na hankad'e kafafuwansa tuni ya zube a wajen,banyi sanya ba na kara dauka na kwala mishi a goshi. Ihun daya fasa yayi daidai da shigowar Hamza da Usman da Nura. Tsayawa nayi ina huci da fada"Wallahi gobe ma ka k'ara gigin b'atamin aikina sai nayi maka abunda yafi wannan haka kawai..." Hannu Hamza ya daga da niyyar kwad'eni ga mamakina Usman ya rikeshi,bani kadai ba dukkansu suma sunyi mamaki hatta da Raliya dasu Hamida da suka fito. "Kana da hankali kuwa? Sakarmin hannu!" Usman shima yace"Meyasa kake da son kaine Hamza?(Kasancewar raini ya shiga tsakaninsu bama kadan ba) Baka ganin laifin na dan banzan yaron nan ne da har zakayi gigin marin Tasleem? Wannan ma ai son kaine." Ya saki hannunsa,ya dubeni "Ke wuce ki tafi." Na dauki mop da robar zan fita,Nura ya dakamin tsawar data firgitani,ya iso ya janyo rigata wannan yasa na fadi na zubda ruwan,ba karamin buguwa k'uguna yayi ba. Kukana ya tsaya sa'ilin da Usman ya daga hannu ya mari Nura. Dakin yayi dif,ya cakumi wuyansa "Wallahi ka kara gangancin taba lafiyarta saika raina kanka! Metayi maka?!" Nura ya fisge hannun Usman daga wuyansa "Nika mara akan wannan yar iskar?" "An mareka!!" Nura yayi kwafa ya fice a fusace. "Hamza bimin bayansa kada ka bari ya dawo nan." Cewar Raliya sanin halin dabancin Nura don ba karamin aikinsa bane ya dawo da wuka ko wani makamin. Hamza ba musu ya fice. Raliya ta dawo gaban Usman "Meke yawo a kwakwalwarka?! Akan wannan yar iskar ka daki kaninka abunda baka tabayi ba shekara da shekaru sai yanzu da girmanku da komai?! Me ta baka kaci?!" Bai saurareta ba ya dawo gabana ya dagani "Sannu Tasleem,tafi zansa a goge." "Uban wa zakasa aikin? Wallahi kaji na rantse maka idan baka fita harkar shegiyar nan ba ranka zai mummunan baci. Dawo ki gogemin waje!" Ta dakamin tsawa,ina hawaye na sunkuya dakyar zan dauki robar saboda zafin buguwar da nayi saidai Usman ya rigani ya dauka ya mikomin. "Kiyi a hankali." Raliya ta sanyashi ficewa na lura baiso hakan ba,haka nayi aikin nan ina mamakin abunda ya faru. Tun daga wannan ranar kuma sai na soma sakewa Usman kadan kadan,nakan gaisheshi hakanan nakan je dukkan wani aiken da zaiyimin zuwa gidansa ko kicin din Raliya da sauransu. Ban dai sakarmishi sosai ba,amma babu wannan rainin sosai. Har kuwa zuwa lokacin bai rabu da fita yawon dare ba. Nasha ganin Meena tazo wajen Raliya tana bala'i akan ita ta soma gajiya da bin mata irin na Usman,mutum tamkar wanda aka yiwa asiri. Raliya saidai ta bata hakuri don babu laifi iyayen meena akwai naira hakanan takan lasawa Raliya sosai domin ita din macece wacce bata godiya ga Allah. Duk da irin arzikin da ta hau kai tayi zaune na Abba,ga kuma business da takeyi,hakan bai hanata hangen na wasu ba. Bayan watanni uku,lokacin Mamma ta kusa shekara a gidansu,kawai na tsinci wayar Yaya musty yana yimin albishir cewar an daurawa Mammana aure da wani almajirin Malam. Har tsalle nayi don murna. Yara da yawa sukanyi bakin ciki idan uwarsu zatayi wani auren alhalin ubansu na raye, kai koda ace baya raye akwai yaran dake taya ubansu kishi amma nikam baruwana ko a jikina. Daga dariya kuma sai na fashe da kuka. Ina cewa shine ko a gayamin nazo da wuri? Dariya yayi yace kada na damu anan Kazaure Mamma zata zauna duk sanda naga dama na tambayi Abba ya barni toh nazo na ganta. Naji dadi kwarai ya kara tambayata game da Yaya abdullah nace mishi sauran mishi watanni uku kawai ya dawo. Daga haka mukayi sallama tare da alkawarin idan yaje gidan zai kirani mu gaisa da Mamma. Ai kuwa ko awa biyu ba'ayi ba yayi kirana,na hau bud'a karshe na saki dariya. Nayi mamaki dana ji muryar Mamma a sanyaye har na tambayeta ko bata farinciki da auren nan? Bata bani amsa ba ta share da tambayar lafiyata. Nace alhamdulillah,tace zan cigaba da karatune? Na tabe baki "Bansani ba Mamma." "Kamar ya baki sani ba Tasleem? Keda mahaifinki? Kije kiyi mishi magana tun lokaci bai kure maki ba." Na amsa da toh saidai kuma abunda Mamma batasani ba shine,idan har sai naje ga Abba na gwammace nayita zama haka a gidan. Haka mukayi sallama da ita. Bayan kwana biyu,Meena matar Yaya Usman ta haife tsohon cikinta ta samu d'iya mace. Murna a wajen yan gidan ba'a magana. Nikam ko ajikina daman ba wani mutuncinsu nake gani ba. ******* Bayan kwana uku da haihuwar meena,misalin biyar na yamma,ina zaune a bakin firij na Raliya ina gogewa,ita kuwa da yaranta suna falon suna kallon wasan Hausa saidai ko inda suke bana kalla ballantana film din da suke kallo ya dauki hankalina don tun fil'azal fina finan hausa ba burgeni sukeyi ba barni da da kallon Indian series da Korea anan kam ko makiyina ke kallo zan saci kallo. Sallamar Usman ta katsesu,Hamid bai amsa ba saima ya mike ya fice saboda a yanzu haushinsa yakeji akaina. Bayan su hamida sun gaisheshi ya dubi Raliya. "Wa kike ganin ya dace ta zauna wajen Meena ne?" Yayi maganar tamkar da sa'arsa,Raliya bata ko damu ba ta kyabe baki "A'a toh,ko Dijangala ai sai ta zauna. Idan kuwa batason aikinta ga waccan tsiyar saiku kwasa." Sai lokacin na dubeta kafin na watsawa Usman mugun kallo wanda na jima banyi mishi irinsa ba. Murmushi yayi ya dubi Raliya "A'a dijangala shiririta ne da ita,tunda dai ga gwaggon meena zata dunga yi musu wanka sai Tasleem ta dunga gyare gyarem gidan." Raliya bata musa ba domin duk yanda zan kuntata a rayuwa shi tafi kauna. Tace "Hakan ma yayi,ke! Idan kin kammala ki tattaro kayanki ki koma gidan Usman har sai matarsa ta gama wanka sannan zaki dawo." Bance uffan ba don bakin ciki,a matukar fusata ta kammala aikin na mike na shiga daki. Haka na tattaro kayan na fito. Hamida mukayi arba da ita ta tuntsire da dariya gami da yimin gwalo"Haka zaki k'are." Kamar nace mata wani abu saidai na fasa nayi gaba,Raliya har lokacin tana falon banko kalleta ba nayi gaba abina a fusace. Saida nazo daidai garden na zube anan na fashe da kuka,wai haka rayuwata zata k'are? Wane irin uba gareni da bai daukeni komai ba? Ya manta da ya haifeni ne har ya banzatar dani a gidansa ya maidani wofi? Ace yan aiki ma sun fini daraja da kima a gidannan? Na daga kaina nakai duba da d'an lilon da muka saba wasa da Yayana. Haka zaiyita cillani yana goyani muna zagaye garden dinnan muna dariya. Ba zato naji an dafani ta baya,nayi azamar juyowa ganin Usman bansan lokacin da naja tsaki ba nayi kokarin mikewa yayi saurin dawowa ta gabana. "Haba Tasleem,ashe tsanar da kika yimin har takai ace kije ki taimakawa matata ki zauna kina kuka? Duk cikinmu waye mai tausayinki bayan ni? Haba Tasleem,banji dadi ba wallahi." Ganin yanayin fuskarsa sai naga kamar ban kyauta ba,nace "Ni ba gidanka ko matarka na tsana ba ai,irin wannan rainin hankalin da akeyimin a gidan ubana ne na kasa gane dalilinsa. Bansan kuma me na tsarewa mutane ba." Na karashe cikin tsiwa,yayi dariya ya kawo hannu zai dora kan lebbana nayi azamar ja da baya,cikin tsoron yanayin kallon da yakemin "Tasleem komai naki abun sha'awa ne wallahi. Ni bana k'inki,inason ganin kanwata a kusa dani shine ma dalilin da yasa na nemi alfarmar zuwanki. Kiyi hakuri inajin dadin yanda kika kware a gyara muhalli. Meena KAZAMAR GIDA ce, banason ganin gidan nan da kazanta. Don Allah kanwata wallahi tana yin arba'in I promise you zaki komo gida." Bance komai ba na mike na dauki jakata nayi gaba yana magana ko juyowa banyi,menene saukin da nan da can din? **** Baby ta numfasa,hawayenta ya karu wani yana bin wani. Haris ya miko mata (handkerchief) dinsa,tasa hannu ta karb'a saidai bata da niyyar share hawayen. Ta dubi Haris wanda shima ya gaji da waigenta ya karkato gaba daya yana duban fuskarta don jin dadin hirar. "Haris a wannan zuwan nawa ne gidan Usman komai na rayuwata ya soma tabarbarewa. Yanda akayi kuwa shine......." 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (34) "Usman ya dunga jana a jiki da wasa da dariya musamman idan ba idon matarsa a wajen. Tun ina daure masa har dai na hakikance dagaske tausayina yakeji kuma kauna ta don Allah yakemin. Hakan ya zamana na amince cewar bashi da wata manufa akaina. Yaya Abdullah kuwa munfi sati lokacin bamuyi magana dashi ba don bana samun kudin da zan sayi data,hakanan shima bansan meya hanashi kirana ba. Wahala iri iri babu banayi a hannu meena,ni ce kula da jaririyarta da taci sunan uwar meena wato Sadiya suke kiranta da Ummi. A farko Usman so yayi ya sanya sunan mahaifiyarsa saidai ta murje idanunta tace sam bazata amince ba,UWA TAFI UWA don haka saidai a sanya sunan nata uwar. Haka dai Usman ya goyi bayanta,dayake itama Raliyar irin dukiyar da ake kawowa Meena daga gidansu a matsayinta na wacce ta haifi jikar fari ya hargitsa mata kai tace bakomai abi tsarin da Meena da takeso. Wanki kuwa babu ranar da hannuna baya taba ruwa,hakanan daidai da undies din Meena ni nake aikin wanke mata su. Sau daya na taba gigin yi mata musu akan wankin ta jibgeni ba tare da kowa yayi yunkurin cetona ba. Hakanan nayi jinyata na warke domin alokacin Usman baya garin yaje daurin auren abokinsa a Zaria kamar yanda ya shaidamin. Bakar ranar da bazan mance ba itace ranar da babu kowa a sashen usman sai ni. Gwaggo ta raka meena asibiti don allurar da zata kai Ummi,ina zaune a falo zaune kan kujera ina hutawa sanin da nayi matar gidan batanan balle kuma ta gani tunda dai ta rigaya ta sanyamin dokar hawa kujerunta nikam gajiya da aikin dana kammala yasa na shimfide saman kujerar ina kallon tashar Zeeworld da suke hasko series dinnan na Destiny wanda an riga anyimin nisa sakamakon jimawa da nayi ban kalla ba. Yawo naji wani abu kamar hannu yana yimin a kunnena nayi azamar mikewa zaune don ba karamin firgita nayi ba. Ganin Usman yasa nayi murmushi kadan ban kawo komai a raina ba na gaisheshi hade da tambayar "Yaushe ka shigo?" Wani kallo yake watsomin,hakan yasa cike da mamaki na dubi shigar dake jikina naga babu inda na kuskuro da shigar banza. Na kara dubansa "Lafiya dai baban ummi?" Ya basar yana mai mikewa tsaye da dariya "Lafiyar kenan Kanwata,kallonki nakeyi ina tausayawa rayuwarki. Ace ke kam baki da wani hutu sai masu gidan basunan kike da yancin sakewa tamkar ba gidan mahaifinki ba?" Nayi murmushi ina mai jin dadin yanda Usman ke nuna damuwarsa akaina,alokacin na ayyana cewar ko na manta kowa bazan mance kaunar da Usman ya nunamin ba alokacin da dukkan gidan suka juyamin baya. "Ayya,bakomai Baban ummi wataran sai labari fa." Yayi dariya yace "Hakane kanwata,kiyi kallo abinki domin kuwa ina maki albishir cewar matar gidan bazata shigo yanzu ba don zata biya ta gidansu." Naji wani sanyin dadi shi kuwa yayo hanyar dakinsa na maida kaina ga kallo. Jimawa kadan ya fito ya shiga kicin bayan ya chanja suturar jikinsa zuwa doguwar jallabiya. Ban damu da sanin abunda zai aikata a kicin ba,a cewata ma,ai gwara kada ya matsamin ya barni na dan huta kafin hakimar tasa ta dawo. Hankalina ya nutsa sosai ga kallo saidai naji alamar ajiye kwalin a kusa dani. Hakan yasa na juyo na dubeshi,murmushi ya sakarmin yana kurbar lemon kwalin na Chi exotic dake hamnunsa,yayimin nuni da ido ga lemon da yake ajiye akan tebur kusa dani. "Bismillah kina kallona,nasan rowa irin ta Meena bazaisa ta baki damar daukar abun sha ba. Bari na dan kwanta kafin nan da la'asar." Ya mike ya shige daki,nayi murmushi don nasan gaskiya ya fada. Meena rowan tsiya ne da ita,koda bak'i tayi sai sun nemi ruwa sannan ake basu balle akaima ga lemo. Na dubi kwalin lemun ina tunanin yaushe ma rabona dana samu yancin shan lemun kwali duk da a baya katon katon babu irin wanda Abba baya ajiyewa Mamma. Na dauka na bude na sha sosai,inayi ina kallo. Tsayawa nayi cak yayinda kaina yayimin nauyi,na ajiye kwalin lemun na dafe kaina ina mai runtse ido. A hankali na soma fita hayyacina,tun ina jiyo muryoyin dake fitowa a tv har dai na daina ji da ganin komai." ***** Baby ta dakata tana mai sheshshekar kuka sosai,Haris cike da tausayawa ya daure yace "Kiyi hakuri Tasleem." Kamar bazatayi shiru ba,har ta soma rikita mishi tunani don hakikanin gaskiya ya tsani kukan mace. Dakyar ta nutsu ta goge fuskarta da (handkerchief) din daya bata. Kafin ta zubamishi jajayen idanunta wadanda sukayi kusan kwana uku suna zubar da ruwan hawaye.[2/3, 21:29] Rufy: 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (35) "Haris a wannan ranar Usman ya ketamin haddina. Yayi amfani dani ba a hayyacina ba." Ta numfasa kafin ta cigaba "Baccin nan bai sakeni ba sai wajen magriba. Nayi mamakin irin radadin da naji a gabana. Na yunkura da zummar mikewa daga shimfidar da nake kwana na katifa a karamin dakin yar aikin meena wacce zuwana yasa ta koma sashen raliya da aiki,saidai ko kalilan ban iya motsawa ba. Kawai sai na fashe da matsanancin kuka,a hankali kuma tunanina ya dawo da lemun dana sha hakanan cikin magagin bacci na hango fuskar Usman lokacin daya kwasheni zuwa dakina. Nayi azamar duba pant dina,jinin dana gani ba karamin dagamin hankali yayi ba. Ihu nasa hadi da fashewa da kuka. Yayi daidai da shigowar Meena da Gwaggonta,wuf suka fado dakin. Meena na fadin "Wane irin iskancin banza ne zaki...." Sauran maganarta ta makale ganin halin da nake ciki,gwaggo ta matso tana buga salati "Mun shiga uku,Aminatu kinga abunda nake gani? Yau tsinanniyar nan ta janyo mana abun magana." Meena ta dubi Gwaggo tace"Wa?! Wallahi badai dani ba! Kanta ta janyowa,karuwae banza da wofi. Bazaki janyomin zagin mutane ba." Daga haka ta hau buguna kamar Allah Ya aikota. Ihu nakeyi ina kuka kakkarfa saboda radadin daya hademin biyu. Ta sakeni tayi wuf ta fita ina nan zaune ina jan jikina zan shiga bandaki ta dawo rike da bokiti,kafin na ankara ta gwalemin kafafuna ta watsamin. Ai bansan sadda na saki razananniyar k'ara ba saboda azabar ruwan zafin nan,daga haka na sume. Ban farka ba sai a gadon asibiti. Nayi mamakin ganin har da Abba cikin wadanda ke tsaye a kaina,sai Raliya da kuma Gwaggon Meena. Na dubesu daya daya kafin na maida dubana ga Abba cikin matsanancin tsanarsa. Dukkansu babu masoyina ciki,makiyana ne. Bansan me suka kawoni ayimin ba bayan sun rigaya sun gama da rayuwata,inama ace sun barni na karasa rayuwata anan. Na kauda kaina ina mai jin saukin radadin azabar da nakeji a gabana bansani ba ashe wai har dinki akayimin. "Munafuka,ke juya keyarki mana kin jawo mana zagin mutanen gari. Haba Tasleem,me muka rageki dashi da har sai kinje ga bibiyar yan iskan gari? Har nawa suka baki kika basu kanki? Tir!" Cewar Raliya tana matsar kwallar munafunci. Bance uffan ba,jira nake naji abunda zai fito daga bakin Abba saidai baice komai ba fuskarsa cike da bacin rai ya nufi hanyar ficewa. "A'a Doctor ina zakaje kuma?" Cikin takaici ya fice baiko k'ara kallonmu ba. Yana fita itama Gwaggon Meena tace zata koma gida don ba aikin kula dani ya kawota gidan ba. Bayan fitarta Raliya ta tuntsire da dariya harda hawaye,idona na runtse inaji kamar na mike na janyota na d'irka. Naji maganarta daf dani "Usman ya biyani! Da ace tun farko nasan kudurin nan yayi a kanki da tuni na bashi goyon baya hakanan da banji bacin ran kulaki da ya dungayi ba. Ki godewa Allah ma da abun ya tsaya a iya nan. Na tsaneki! Na tsani uwarki da dukkan tsatsonta! Nafison ganina da ya yana kadai a gidan ubanki.! Sai kiyi jinyar kanki!" Ta kara tuntsirewa da dariya ta juya zata fita, wallahi bansan lokacin dana fisgota ba na janyo almakashin dake ajiye cikin tasa a gefen kaina. Saitin wuyanta na sanya kafin na soma magana a fusace "Kina zaton kinci galabar abunda kikayimin ko? Toh wallahi ki ajiye a ranki saina dauki fansa akan Usman! Sai ya gane shayi ma ruwa ne RALIYA! Don ina shanye dukkan wahalhalun da kuke sanyani ba wai hakan yana nufin tsoronku nakeji ba! Kawai dai biyayya nakeyi ga MAHAIFIYATA! Wallahi ko ba dade ko ba jima sai na dauki FANSA.!" Na wuncikalar da ita,na ajiye almakashin,a fusace tayo kaina wanda hakan yayi daidai da shigowar nos. Ba don taso ba ta bini da mugun kallo,na tabbata tayi mamakin karfin hali irin nawa,da shekarunta da komai nayi mata haka? Hum, bari dai akai mutum bango Haris, wani abun da bai taba zaton zai aikata ba sai ya aikatashi. Kwanana uku a asibitin Abba,wata nos me mutunci ke kula da lafiyata bansani ba ko bisa umarnin Abban ne kodai a'a. Ni nake lallabawa nayi wankana nasa sutura. A rana ta hud'u ne ina zaune ina shan lemun b'awo naji sallamar wanda banyi tsammanin ganinsa nan kusa ba. YAYA ABDULLAH. Gaba daya ya chanja yayi haske,saidai fa ya rame akan yanda naga hotonsa kwanakin baya. Sanye yake da shirt da wandon jeans bak'i ya dora brown jacket a samanta. Farin cikin ganinsa ya koma ciki sakamakon yanayin dana gani a fuskarsa. Kallon da yakeyimin ba karamin kad'amin 'yan hanji sukayi ba. Salati na shigayi a zuci kafin na russunar da kaina sai hawaye....... 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (36) Karasowa yayi ya durkusa a gabana,hannuna ya riko na hagu kafin ya fashe da kuka. Hankalina ya tashi ainun ganin kukan Yaya abdullah tamkar na wani karamin yaro. Saidai ban iya cewa uffan ba nima sai karfin kukana daya k'aru. Na ajiye lemun b'awon dake hannuna. Ya dawo ya dubeni cikin rawar murya yace "Why Tasleem? Why?! Meyasa kika bari rayuwarki ta lalace har haka? Wane irin halin rashi kike ciki da har zaki bawa wani kanki? Meyasa Tasleem? Akan wane dalili kika boyemin rashin Mamma a gidan nan?" Ya karashe cikin sheshahekar kuka. Na tsayar da idanuna bana ko iya kiftasu a kansa, bakina a bude na kasa cewa komai. Tsananin mamakin yanda akayi yayana jinina ya yarda da wannan kazafin da akayimin nakeyi. Ashe Yaya abdullah shima zai amince da wannan zancen nasu? Ya mike tsaye ya zauna gefen gadon,na cigaba da bin fuskarsa da kallo yayinda ya dauke kansa yana mai kara tamkemin fuska. Murmushin bakin ciki nayi,tabbas an rabani da yayana kuma dan uwana. Babu sauran wata magana,banga amfanin sanar dashi komai dangane da lamarina ba. Babu wani amfani a yin hakan. Zuciya irin tawa tasa nak'i bayyanawa Yayana gaskiyar abunda na sani. Maganarsa ta katseni "Nayi bakin cikin jin rabuwar Abba da Mamma. Kodayake naga alamar akwai wata a kasa tun rayuwar da nayi a abroad. Wallahi Abba baida masaniyar a yanda na kammala karatuna na dawo. Duk a zatona Mamma tana tare da Abbana,wannan yasa nayi kiranta na shaida mata dukkan halin da nake ciki,bani da komai sannan na tabbatar idan a wannan gab'ar nace zan ajiye karatuna na dawo toh fa nan ma wata matsalarce don bani da kudin jirgi. Mamma hankalinta ya tashi tace kada na sake nayi kokarin tahowa na bata nan da kwana uku. Haka na cigaba da zama a gidan yayan abokina,Rilwan da muke makaranta tare. Har saida ya zamana inajin nauyinsu,gani nakeyi kamar ina matsa musu. Rilwan ya fahimci halin da nake ciki domin ya lura har lokacin bani da niyyar biyan kudin makaranta. Bansan ya akayi ba sai ji nayi yace na shirya na rakashi wani waje. Ban kawo komai ba nayi shirina tsaf muka tafi. Nayi mamakin ganin Rilwan ya biyamin kudaden nan,bawai ina mamakin ko a ina ya samu kudaden nan bane,ko kadan saboda nasan waye mahaifin Rilwan. Babban ma'aikaci ne a 9ja garin Abuja. Mamakin da nakeyi har wane matsayi Rilwan ya bani da sai biyamin kudin shekara biyun daya ragemin. Na rasa kalmar daya kamata na godemishi. Har hawayen farin ciki nayi,ya nunamin babu komai domin shi don Allah yake sona. A haka bayan kwana uku sai gashi Mamma ta turomin kudi har dubu dari uku. Nayi mamaki sosai,a karshe nayi kiranta na shaida mata yanda akayi,kusan ta fini murna tace na tattala wadannan zasuyimin amfani kada na damu Abba ayyuka sukayimishi yawa shiyasa naji shiru. Na bita a haka. Kinji yanda na kammala karatuna,da taimakon Rilwan da Mamma sai matar da nake niyyar aura, Hasinat kamar yanda kika san tsakanina da ita. Ita kam dukkan wani abu daya danganci sutura da kayan kamshi ita ke siyamin batare dana sanyata ba. Tun bana shiga harkarta har nazo ina shiga,iyayenta sun sani hakanan mamanta na yawan waya da Mamma. Itama hasinat tasan mamma sosai." Yaya abdullah ya numfasa ya share hawayensa yana dubana cikin mugun takaici "Na kammala na dawo saina riski labari marar dadin ji daga bakin Maman twins(Raliya),wai Tasleem kin siyar da mutuncinki saboda abun duniya?!! Wane irin kunci kika shiga?!! Abba ya cucemu daya dauke mana mahaifiyarmu daga gidansa!" Zuwa lokacin hawayena sun gaji da zuba sun dauke,murmushi kawai nakeyi wanda yafi kuka ciwo "Kaddarata ce mai yiwuwa! Haka nawa..." "Ba kaddara bace!!" Ya katseni a tsawance har na firgita ina dubansa yanda ya mike cikin fusata. "Son zuciyarki kika bi tasleem! Kin manta tarbiyyar da Mamma ta jima tana iyakar kokarinta wajen baki? Meyasa zaki lalata rayuwarki har haka? Nayi bakin ciki marar iyaka jin wannan batu! Nayi danasanin tafiyata na barki,wallahi da nasan Abba zai rabu da Mamma da ban amince na ketara ko nan da can ba!" Ya dakata yana mai hade kansa da bango kafin yayi wuf ya fice, ina kiransa saidai ko waigowa baiyiba. Kaina na cusa cikin filo ina kuka mai karfi. Gaba daya zaman asibitin ya isheni hakan yasa na sauko na dauki hijabin da bansan ko na waye ba,dashi dai nakeyin salla,ban iske takalmi ba hakanan na fice. Ban tsaya ko'ina ba sai kofar gidanmu,na nemi rance wajen baba Maigadi don bawa mai adaidaita,baba maigadi yace babu komai naje zai sallameshi. Yayimin sannu banko tsaya amsawa ba nayi ciki. Tsayawa nayi cak ina duban ko'ina na gidan,ina ya dace na nufa? Wajen wa zanje? Waye zai saurareni? Na kara taku daya biyu,na daga da niyyar yin na uku mukayi ido hudu dashi,cikin sanyin jiki na maida kafar baya na dukar da kaina. Ya k'araso a fusace "Me kika dawo kiyimin?!!!" Na dago kaina murya na rawa na soma magana "Abb..." Marin daya saukemin a fuskata ya dakatar dani daga karasawa "Fitarmin daga gida,yar iskar yarinya! Kin bata wayonki! Bazaki zo ki b'atamin tarbiyyar yarana ba! Shegiya! Kedai kam ina kwakwanto akanki! Anya nine ubanki?!!!" "Wannan shine furuci na biyu cikin ukun da bazan taba daina tuna su ba,hakanan tunaninsu ya sanyani yin mummunan hatsarin da har ka kaini asibiti Haris." Cewar Baby tana duban Haris,sannan ta cigaba. Kalaman Abba yayi daidai da fitowar yayana Abdullah a guje daga sashen Mamma. Gwuiwoyinsa a k'asa ya shiga rokon Abba akan yayimin afuwa ya barni na rayu koda a sashen 'yan aiki ne. Abba ya hankad'ashi "Gidana ne! Ina ajiye wanda naso a ciki amma banda yan iska! Kaima kuma idan bakayi wasa ba yanzun nan zaka bita ku tafi." Maganar da Abba keyi da karfi ce ta janyo hankulan yan aiki. Zuciya ta kwasheni cikin kuka da daga murya nace "Naji gidanka ne! Zan fita na barshi,zan barshi har abada!! Kai uba ne ga wasu amma ba ni ba! Na amince idan har ka manta hakkina dake kanka ka manta akwai hisabi a tsakaninmu! Toh hakika zan bar gidanka yanzu ba anjima ba. Ko a kiyama bana fatan Allah Ya kara hadani da azzalumin uba..." Mari Yaya abdullah ya daukeni dashi, "Kina hayyacinki kuwa? Kin manta waye agareki?!!" Cikin kuka da daga murya nace "Ban manta ba yaya abdullah! Amma shi ya mance diya nake awajensa. Abba ina kake sadda nake rayuwar garari acikin gidan ka?! Ina kake sadda abincin yan aiki ma yafi nawa mutunci da dadi a harshe? Ina kake sadda na kammala karatu?!! Ka taba zaunar dani kaji damuwata?! Ka taba yimin nasiha koda sau daya akan rike addinina?! Ka taba damuwa da ni?! Wallahi na tabbatar ko sunana bazaka iya tunawa ba saboda baka sona! Ka tsaneni! Har gashi ayau kana kokwanto ko kaine ubana!!! Shikenan gaka ga gidan naka! Allah zai mana sakayya!!" Daga haka nayi waje a guje,Yaya abdullah yana kirana amma ko juyowa banyiba. Nayi nisa sosai da gidanmu kafin na samu kasan bishiya na zube ina kuka da numfarfashi. Kaicona!!!! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (37) Taku naji da sauri sauri kafin aci burki a gabana. Na dago kaina,Yaya abdullah ne. Kaina na cusa cikin cinyoyina,dagomin kai yayi kafin ya rungumeni shi kansa hawayen yake. Ganin mutane sun soma taruwa ne yasa ya mikar dani tsaye yaja hannuna. Na turje na tsaya cak, ya dubeni na girgiza kaina "Kayi hakuri yaya,bazan koma gidan nan ba." Ya dan dubi mutanen da suka taru kafin ya sassauta muryarsa "Nima ba nan zan kaiki ba,biyoni kawai." Adaidaita sahu ya tarar mana muka shiga. Har lokacin jikina kakkarwa yakeyi ga hawaye wani yana bin wani. "Duk da laifin da kika aikata Tasleem,I can't change the fact that you are my blood sister. Bazan iya bari rayuwarki ta tagayyara ba Tasleem. Abba mahaifinmu ne,a yanda Mamma ta koyamin tace duk runtsi da tsanani kada na gujeshi wataran sai labari. Zan kaiki inda nasan zaki zauna cikin aminci har zuwa lokacin da Abba zai sakko ya yafemaki. Amma bayan da na samu labarin Mamma tayi aure bazan amince da zuwanki Kazaure ba har ki dagamata hankali." Tunda ya soma maganganun hankalina yana ga waje, sai alokacin na waigo na dubeshi. Kallonshi nakeyi kamar wata tab'abb'iya ina mamakin yanda Yaya abdullah ya hakikance cewar na aikata zina da gangan. Murmushi nayi alokacin da ruwan hawaye ya malalo kan hancina. Na yarda sharrin mace yafi na shaidan. Usman!! Shine wanda ya fadomin a raina,kwarai ya tafka babban kuskure a rayuwa tunda yayi gangancin yimin wannan ta'asar,nasha alwashin daukar FANSA. Unguwar tarauni,anan muka yada zango,yaya abdullah yayita yiwa mai adaidaitan nuni,har a karshe muka tsaya a wani gida karami na sumunti saidai babu ko fenti. Muka fito ina ta kallon gidan kallon rashin sani. "Muje." Ya katsemin tunani bayan yace mai adaidaitan yayi tsumayinshi. Yace na soma shiga. Na shiga da sallama,matar dake zaune ta juya baya tana alwala ta waigo tana amsawa. Ganin Kulu yasa naje a guje itama ta mike da azama na rungumeta na fashe da kuka sosai. Tun tana farin cikin ganina har dai jikinta yayi sanyi,sallamar Yaya abdullah ta katseta daga tambayar da take shirin jefomin. Ta sakeni tana "Lale marhabin da d'ana. Saukar yaushe?" Yayi murmushi yana kokarin mayarda kwallarsa,ta dubeni ta dubeshi a sanyaye tace"Lafiya kuwa d'ana? Menene ya faru?" Kafin muce wani abu tayi daki tana fadin"Ina zuwa." Ta fito dauke da tabarma ta shimfida. Bayan mun zauna yaya abdullah ya dubeta "Nayi bakin cikin dawowa naga bakya gidan Kulu,kamar yanda mutuwar auren Mamma ya tayarmin da hankali. Saidai tunda a yanzu tayi aure mun dauki hakan matsayin KADDARA." Kulu wacce tun soma maganarsa taji babu dadi saidai furucinsa na karshe ya dan sanya ta saki fuska"Kai Hajiya tayi aure? Toh ai Alhamdulillah. Kada ka damu dana karatun da kakeyi ne yasa ba'a bari labarin ya riskeka ba amma komai na Allah ai mai kyau ne." Ya gyada kai"Hakane." Ya danyi shiru kafin yace"Kulu nazo neman karamar alfarma a..." "Fadi ko menene D'ana,babu abunda banajin zaka nema da nayi maka na kasa yinsa." Ya numfasa yana murmushi"So nakeyi ki rikemin amanar Tasleem zuwa nan da wani lokaci......" Kulu taji abun banbarakwai,koda ta nemi dalili. Ya sanar mata Abba ya baya gari shine matsi da wahalarwa suka sanyani nayi kokarin guduwa shine ya yanke gwara ya kawoni gabanta na zauna. Jin abunda yace yasa na kalleshi kwalla ta cikamin ido,yayimin alamar cewar kada nace komai sai kawai na sunkuyar da kaina har mamakin yanda Yaya abdullah ke son kare laifin Abba nakeyi. Wane irin zuciya ce dashi har haka? Kulu ta hakikance sanin halin Raliya zata aikata abunda yafi haka acewarta,irin hakan ke sa yaro ya shiga duniya. Yayi mana sallama bayan ya tabbatar min zai sanya mai adaidaita sahun nan ya kawomin kayana banko kalleshi ba ya lura fushi nakeyi dashi. Bai kulani ba yayi gaba,wajejan yamma sai ga mai adaidaitan ya kawo jakar kayana,ciki kuwa koda na bude na samu dubu goma a samansa. Damkasu nayi gaba daya ga Kulu. Muna hira take shaidamin cewar da matar d'anta suke zaune da yaransu amma yanzu sunje ganin gida acan Ringim. Na nuna mata babu matsala zan iya zama. Na lura a zamanmu tana son takura kanta akan lallai sai tayimin cima mai dadi. Saida na nuna mata banaso zan iya irin rayuwarta sannan ta hakura. Satinmu biyu tare,Salamatu da yaranta uku da mijinta suka dawo. Sunyi mamakin ganin bakuwar fuska,saida Kulu ta fahimtar da d'anta Salmanu ko ni wacece tukunna. Nan da nan kuma naga fuskar Salamatu ta chanja har ta kasa boyewa tace wai Baba ta fiye yi musu kwashe kwashe alhalin daman da yaya suke rayuwar? Kulu dai jiki yayi sanyi don ba ranar ta soma ganin rashin arziki wajen Salamatu ba hakanan d'anta kansa yana shayin matar tasa. Nidai bance musu uffan ba. Rayuwata tana cigaba da tafiya a wajen kulu da dadi babu dadi,Yaya abdullah baya wuce sati baizo ba kafin kuma ya dauke kafa yaje Kazaure. Nan ma daya dawo ya tahomin da tsarabe tsarabe duk daga yan uwa. Banyi wani murna ba tunda dai da nayi mishi korafin tafiya dani ya nunamin kamar bayason kaini a yanzu,na lura kyamata kawai yakeyi. Watana uku a gidan,lokacin cikin hukuncin Allah takardun Yaya abdullah sun kammalu har ma da taimakon abokinsa Rilwan ta samu aiki a wani kamfanin mahaifin Rilwan na Abuja,suka bashi karamin gida da motar kamfaninsu. Koda ya dawo ya sanarmin nayi mishi murna saidai lokacin bani da cikakkiyar lafiya. Kullum cikin zazzabi nake ga kasalar jiki. Ya kwasheni ni kadai a mashin dinsa mukaje asibiti. Koda mukaje likita ta nemi fitsarina,a tsorace na mike naje nayi na mika lab. Muna nan zaune jiki a sanyaye har aka kammala aka bamu result muka kai ga likita. Ta dago tana murmushi "Congrats, you are pregnant." Ihu na fasa na zube a wajen ban kara sanin meke wakana ba saidai na farka na ganni kwance a gado. Likita na tattaba goshina,tunawa da nayi da abunda naji a karshe yasa na kara sakin ihu ina fadin "Wallahi saikin zubarmin! Banaso!! Wallahi ..." Yaya abdullah ya toshemin baki yana kuka "Kin ja mana Tasleem! Baki kyauta mana ba." Likita dai sannu take bina dashi. Bayan mun fito Yaya abdullah yace bazai iya barina kuma a hannun kulu ba,dole dani zai koma Abuja ba yanda zai iya. Nidai babu bakin magana illa bakin cikin dake nukurkusata ya zamana daidai da shi kansa haushinsa nakeji. Naji duniyar na tsani kowa da komai. Mahaifiyata kadai ta fadomin a raina,kawai sai na fashe da kukan tausayawa rayuwata. Ya zataji idan tasan abunda ya sameni? Haka dai muka koma mukayi sallama da kulu bayan Yaya ya cikata da kudi yayi mata godiya. Ita kanta salamatu saida ya bata,ba kunya ta karba da rawar jiki. A karshe muka koma ya ajiye mashin din daya aro na makocinmu kuma abokinsa sannan ya tsayar mana da adaidaita sai tasha domin tuni daman kayansa suna tashar a hannun wani amintaccensa. ***** Baby ta tsagaita hadi da jan majina,fuskarta tayi jazur tamkar kosai kamar yanda fuska da fararen kwayar idanun Haris suka sauya launi zuwa ja. Zuwa lokacin shi kanshi hawayen yake fitarwa. Ta cigaba "Haris wannan shine silar zamana a Abuja na shekara daya da watanni a gidan Yayana da matarsa Hasinat." 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (38) Watanmu shida cif a garin Abuja,babu yanda na iya cikina ya girma ya fito so sai. Akan bakin cikin ganinsa ya sanya Yaya abdullah kauracewa yini a gidan,kasancewar estate ne wajen akwai mutane da dama saidai ba wanda ke shiga harkar wani sosai. Kullum rufe nake da hijabi zunb'ulele saboda nauyin da nakeji musamman ma na yayana. Shima baya yini a gidan. Wataranar laraba ne na tashi da matsanancin ciwon mara da baya. Lokacin kuwa karfe uku na rana ga Yaya abdullah bai dawo gidan ba. Sai murkususu nakeyi a tsakar falon ina salati a zuci don bakin nawa ma mutuwa yayi murus. Na rasa yanda zanyi,cikin ikon Allah sai ga Yaya abdullah bayan nakai tsawon awa daya ina abu daya. Jaka da ledar dake a hannunsa ya yasar ya nufoni a guje. "Lafiya tasleem? Haihuwar ce?" Na gyada kai ina runtse ido don babu baki, ya fita a guje ya bude motarsa sannan yazo ya daukeni ya sanyani ciki. Har ya bude motar zai shiga ya dubeni a rikice "Kin hada kayan dana kawo na baby kuwa?" Ban iya magana ba,ya fita da sauri saidai yayi mamakin ganin yanda ya kawomin haka suke a ledar ban fidda komai ba. Ya kinkimo ledar karshe da ya rasa abunyi ya kinkimo harda akwatin kayana kasancewar nak'i jerasu a kwaba don komai ba burgeni yakeyi ba a lokacin. Haka muka isa asibiti,nidai ina motar nan tunda wani azababben ciwo ya murdomin na saki k'ara na sume bansan me ya wakana ba. Bayan farkawata kuwa na ganni kwance a gado wai ashe aiki akayimin aka fiddo jaririn. Saidai kuma baizo da rai ba. Bansan sadda nayi hamdala ba sa'ilin da nos ta shaidamin hakan,ta taimaka ta gyarani tsaf sannan aka chanja min daki. Mintuna kalilan ina nan kwance ina hawayen farin ciki,Yaya abdullah ya shigo da wani wanda kallo daya nayi mishi na fahimci cewa Rilwan ne. Na kauda kaina daga dubansu. Yaya abdullah ya riko hannuna yana murmushi "Sannu kanwata,ya jikin?" Murmushi kawai nayi mishi,kafin shima Rilwan ya matso yana min sannu. Na amsa a nutse, sallamar wata matashiyar budurwa ce ta katsemu. Ta shigo dauke da kwando,a bayanta kuma wani saurayi ne ya tsuke cikin kananun kaya askin kanshi kadai sun wadatar su nunawa mutum irin matasan nan ne masu wankan kwalabo. Suka karaso ciki,nayi yunkurin mikewa da azama naga budurwar ta ajiye kwandon ta iso wajena. "Sorry." Ta fada cikin muryarta na gogaggun yan boko. Ta jinginamin filo na kwantar da bayana akai. A hankali na gaishesu suka amsa min. "Amaryarmu,da alama garin na Abuja yayi maki dadi shiyasa daga sati gashi kin kusa yin wata." Cewar rilwan ya fada yana duban matashiyar nan wacce tuni na daina tunanin inda nasan fuskarta saboda na fahimci itace dai Hasinar Yaya abdullah. Saidai wanda suke tare dinne mai shegen kallo,ban sani ba. Dariyar Hasina ta katsemin tunani "Wai kai ina ruwanka ne? Baka ganin Abdul dina yana jinyar kanwarmu,haka kake so na tafi na barshi duk su wahala? Ayya na manta ma,ban maki gaisuwa ba sister,ya hakurin rashin bebinmu? Allah Yaji kansa." Nayi mamakin yanda Yaya abdullah bai boye musu cewar haihuwa nayi ba,sai duk na tsargu na dauka ya gama sanar dasu dukkan abunda ya shafi rayuwata. "HAYAT kaji kanwar taka ko? Ya kamata ka dunga taka mata burgi irin wannan love haka?" Rilwan ne ya fada ganin ban amsa zancen Hasina ba. Yaya abdullah dai murmushi kawai yakeyi,ta dubesu "Don Allah ku fita kuna matsawa kanwata da hayaniya gashi ko abinci bata ci." Haka suna dariya suka fice, ni kuwa Allah Allah nakeyi su fita saboda bayan tsarguwa da nayi harma da kauracewa mayen kallon da Hayat ke watsomin wanda yana daga cikin abunda na tsana. Hasinat ta hadamin tea ta zubamin chickensoup da suka taho dashi haka ta taimaka ta dunga bani da zafi zafi babu laifi naci sosai. A karshe dai bayan su Yaya sun shigo akayita hira da dariya,nikam kallonsu kawai nakeyi,anan na fahimci cewar an kusa sanya ranar auren Yaya da hasina. Babu laifi na lura tana da mutunci,kamar bazatayi hayaniya ba. Allah Allah nakeyi su fita na tambayi Yaya abdullah abunda ya sanarwa Hasina a kaina. Saidai fa koda suka tafi na tambayeshi,nayi bakin cikin jin cewar ya sanar da ita wai nayi aurena mijina ya rasu ya barni da ciki yanzu ma na haihu d'an babu rai. Koda nayi tunani daga baya na fahimci rufamin asiri yayi. Bayan wata daya da yin hakan,Yaya abdullah yayimin batun komawa makaranta,naji dadi kwarai saidai na nuna mishi ya bari ya kammala hada lefansa tunda a kansa yake. Yayi naam da batuna. Kullum muna waya da Mamma da mutan Kazaure kowannensu na lura a zatonsu ina kano ne basu san cewar ina tare da yayana ba. Gaba daya suna da labarin lefan da Yaya abdullah ke hadawa. Bayan ya kammala ya zaunar dani yace zaije dashi ya kaiwa Raliya ko ba komai tana ganin kimarsa yanzu da yayi kudi amma hakan ba damuwarsa bace shi dai su mika lefansa gidansu Hasinat. Baki kawai na tab'e bance uffan ba. Idan ma ba don Allah take jan yayana a jiki ba ita ya shafa yanzu kam na fidda kaina da lamuran gidansu Yaya Abdullah don ya tashi daga gidanmu. Ranar da aka kai lefa da kayan saka rana ya shaidamin nan da wata uku za'ayi bikinsa. Na tayashi murna. Saidai sabon al'amarin da yake niyyar bullowa cikin rayuwata ya dagamin hankali,banason wata soyayya,asalima ba burgeni takeyi ba alokacin. Amma hakanan Yaya Rilwan ya shiga cusa kansa gareni,tun ina ja baya har dai Yaya abdullah yace kada na damu ya amince da rilwan amininsa ne kada na wulakantashi a hankali sai a rabu. Wannan yasa na sakarwa Yaya rilwan harma nake sauraronsa. Alokacin kuma yayana ya hau gyaran gida bayan ya soma kokarin nemamin admission. Bayan sati uku aka samar min,na soma zuwa nan jami'ar Abuja inda na soma karatuna a fannin shari'ah. BAYAN WATANNI HUDU Anyi auren Yaya Abdullah da anti hasina. Har alokacin sun cinye wata daya suna shan amarcinsu. Tsakanina da Yaya rilwan soyayya ce tsantsa,yana mutuwar kaunata hakanan nima ina sonshi so bana wasa ba. Ana cikin haka kuma na soma jarabawa ta 1st semester ?򚈨a daidai lokacin Yaya abdullah ya dauki hutu zaije Kazaure tare da anti hasina. Har kuka nayi wai dole sai na bisu,ya bani hakuri yace idan na kammala jarabawa sai naje yanzu kam bazasu iya zuwa dani ba. Hakanan na hakura ina ji ina gani sukayi tafiyarsu............" Baby ta dubi Haris "Alokacin kuma KADDARA ta biyu ta afku gareni Haris......! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (39) "Koda dai bazance kaddara ba Haris, nafi jin kunyar nan gab'ar akan na baya domin kuwa a wannan sai ince a hayyacina nake kawai RUD'IN SHAIDAN ne ya jani." Baby ta muskuta tana runtse ido sakamakon gajiyar da hannunta mai rauni yayi. Ta jingina kanta jikin kujera tana mai duban wata mai suyar kosai a gefen titi "Rilwan masoyina ne,wanda ganin irin kusancinsa da Yaya abdullah yasa na saki jiki na hakikance bazai yaudareni ba. Soyayya ta zamani babu irin wacce baya gwadamin. Kayi hakuri da abunda nake fadi Haris, saidai bansan sha'awa ba sai akan Rilwan. Bansan wata soyayyar ba ma sam sai akan Rilwan. Wannan shine babban kuskure dana soma tafkawa a rayuwa. A inda har watarana misalin goma na dare muna hira da Rilwan anan falon gidan kamar yanda muka saba. Shaidan ya rudemu muka aikata b'arna a karo na farko dashi. Sai bayan da komai ya gama afkuwa sannan muka ankara, kuka na fashe dashi ina dukansa ina ihun kiran ya cuceni. A karshe na gudu zuwa daki na kulle,bugu yakemin yana kirana yana mai bani hakuri saidai ina na riga na fita hayyacina. Kukan da bazai dawomin da kima da darajata ba a karo na biyu nayi asara. Dakyar a daren na rarrashi kaina. Nayita istigfari,gaba daya na rame ko makaranta naje bana fahimtar komai na daga tambayoyin da akeyi mana a jarabawa saidai na rubuta abunda na tuna. Ana tashi kuwa a mota har nakai gida ina driving ina kuka. Mantawa nayi ban gayamaka ba,a rayuwar da muka shimfida da Rilwan har tuki ya koyamin motar kanta da nake hawa shine ya siyamin. Yan uwan rilwan suna kaunata,mutane ne marasa daukar kai wani abu. Ko sadda ya siyamin motar banso karb'a ba har ma yayana saida ya yi mishi magana ya nunawa yayanmu wallahi da gaske aurena yakeson yi,kada yayanmu ya damu." Baby ta dubi Haris "Na amince da hakan kuma,saidai zan kira abunda ya faru tsakanina dashi RUDIN SHAIDAN,wannan na daya daga cikin illar kadaicewa tsakanin namiji da macen da ba muharramai ba. Sati biyu da faruwar al'amarin,Yayana suka dawo. Nasha tambaya a wajensu na dalilin ramata saidai na rufesu da cewa rashin lafiya nayi. Suka aminta da hakan. Yayana yana dariya yayimin albishir da samun cikin anti hasina,ihun murna na sanya kafin na rungumeta muna dariya. Ya dakamin tsawa wai nayi a sannu kada na karyamishi mata. Na saketa muna dariya har lokacin. Nasha tsaraba daga Mamma,ciki kuwa harda hotunan graduation dina Yaya musty ya bada aka wanko ya aikomin da Camera dita. Nan na hadasu na adana da wadanda mukayi dasu Mamma ranar birthday dina na sanyasu a akwatina amatsayin tarihi. Rilwan koyaushe cikin rarrashina yake amma sam na daukemishi wuta,kudin da yake turomin ta account har ba'a magana. Ganin abun zaiyi yawa naje na samu yayana da anti suna zaune a falo na fashe da kuka. Hankalinsu ya tashi suka hau tambayata ko lafiya,nan na sanar dashi bayanin kudaden da Rilwan ke aikomin ta account na kara da cewa yayi mishi magana banaso ya daina sannan ya fita hanyata. Sukayi sukayi suji dalilina amma ina saima na kara fashewa da sabon kuka domin lokacin ma shekaruna ashirin da daya(21). Ganin haka yayana yace shikenan zai mishi magana. Bansan yanda sukayi ba saidai kam hankalina ya kwanta sakamakon daina shiga harkata da Rilwan yayi. Ko gidan yazo baya matsawa sai an kirani,amma da zarar ya hangeni ya shiga satar kallona kenan saidai na ja tsaki na harareshi. Hum,yawan samarin da suke biyoni har gida hakanan a makaranta su matsamin yasa yayana kirana yaji ta bakina ko aure nake ra'ayin yi. Nayi azamar cewa a'a yace toh dai na kula domin baison tara samari da nakeyi. Allah Sarki baisan ma basu gabana ba,don har lokacin akwai burbushin son Rilwan a zuciyata duk da tsanar da nakeji nasa a wani gefe na sashen zuciyata. Hum! Bayan watanni uku,mummunan labari ya fito wanda yayi silar rabuwata da yayana da duk wani na jikina......... 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (40) "Ba don Allah Ya kiyaye ba da auren hasina da yayana sai ya mutu. Mummunan labarin kuwa,fitowar ciki a jikina a karo na biyu." Baby ta karashe tana mai jin takaici da tsanar kanta,Haris kansa ya girgiza hakanan yaga bak'in baby anan da har ta kara mikawa wani gangar jikinta duk da dai ta kirayi hakan RUDIN SHAIDAN. Maganarta ta katseshi "Kasalar jiki,yawan bacci da kuma amai da nakeyi ya janyo anti hasina soma tsorata da abunda ta hango a jikina matsayinta na kwararriyar likitar mata kasancewar fannin data karanta kenan. Har take shirin soma aiki a asibitin da Abbanta ke ginawa a garin Abuja. Ta sameni kwance a gadona amai har ya galabaitar dani. Fuskarta a daure cike da tashin hankali ta kirayi sunana. Na dago idanuna na dubeta. "Yaushe rabonki da ganin al'adarki?" Gabana ya bada dam,lallai sai lokacin na ankara da abunda ke shirin faruwa dani. "Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Haris bana fatan na kara ganin wannan ranar,ranar da dan uwan da muka fito ciki daya yayimin dukar kawo wuka kafin ya umarceni da na fice na bar mishi gida." Baby ta fada hawayenta babu ko digon hawaye,muryarta har ta dashe tsabar kukan data sha. "Rabona da period kuwa,tun a watan da Rilwan ya sadu dani. Hum! Ina gayawa anti hasina nakai wata uku rabona da period, sai ta buga salati tana kwalawa yayana kira "My dil! My dil!!" Da gudu Yayana ya shigo,kana ganinsa kasan a firgice yake. "Lafiya?" Ya watso mata tambaya,ni kuwa kuka na sanya don nasan abunda anti hasinat ta gano. Jikina banda kakkarwa ba abunda yake, kafin na ankara tuni ta sanarwa Yaya Abdullah ciki ne dani. Wallahi nan da nan tsikar jikinsa ta tashi,kukan kura yayi ya jawoni ya zare belt din jikinsa yayi ta buguna. Ihu nakeyi ina kuka saidai bai fasa ba. Na tabbata ni ce da laifi. Duk wani zargin da sukayimin a baya cewar karuwanci nakeyi ya fito a bayyane yanzu kam bani da wata mafita. Anan ne yaya abdullah yayi sub'ul da baka da cewa "Shi ne kika kara daukar ciki Tasleem! Kika kara bawa wani kanki?!!! Kin cucemu!" Anan anti hasina tasan cewar cikina na farko ma shege ne. Har tayita hayaniya da fadin ita kam saidai ya maidani gidanmu idan kuwa ba haka ba ita ta fita ta bar mishi gidan. Yaya abdullah ya rasa ya zai ce mata,tuni ta fice ta koma dakinta ya bita ya a bugu amma tak'i bud'ewa. Nikam dakyar na iya mikewa tsaye duk fatata tayi rud'u rud'u tayi jazur. Ina zaune bakin gadona ina kuka da bakin cikin tsanar kaina Yaya abdullah ya k'ara fad'owa d'akin a fusace,jikinsa har rawa yakeyi ya tsaya a kaina. "Kin bani mamaki kanwata,kin bata wayonki. Har da kanki ki dunga kai kanki dakin namiji?!! Tirr da wannan d'abi'a taki. Toh wallahi ki barmin gidana,kuma kika kuskura kikaje ga mahaifiyarmu kika kashe aurenta,wallahi saikin raina kanki! Kije duniya ce! Daidai take da kowa!" **** Baby ta tsagaita anan gami da dafe kanta tayi jim,a karshe kuma kukan ya taho mata ta fashe da kukan sosai,cikin kukan tace "Tell me Haris, ya akeso nayi da rayuwata ne? Ina akeson naje? Mahaifina wanda yayi silar zuwana duniya,wanda shi kadai ne waliyin aurena,shine abun alfaharina,ya koreni daga gidansa yace na fice mishi. A gefe ga yayana wanda muka fito ciki d'aya dashi,komai nawa na damuwa a ganina da hangena ya shafeshi,saidai ashe ba haka bane. Sai gashi da kansa yake yimin korar kare daga gidansa,bayan yayimin kashedin kada naje da mahaifiyarmu! Ina akeso na shiga? Ina akeso naje naji sanyi a duniyar nan? Shakikaina sun gujeni,sun koreni daga wajensu,ya akeso nayi? Waye kuma zai so zama tare dani?" Haris baisan sadda ya janyo hannunta ba ya sanya cikin nashi,alokacin hawayensa sun kasa tsayawa sai zuba sukeyi. Yana son cewa wani abu sai kuma ya fasa gami da sakin hannunta ya janyo handkerchief data ajiye ya mika mata "Kiyi hakuri." Ya fada murya a dusashe. Ta dago kwayar idanunta tana dubansa,yayi amfani da wannan damar ganin bata da niyyar karb'ar handkerchief din ya kai hannu zai share mata fuska,ta rike hannun tana girgiza masa kai kafin ta mayar mishi da hannun kasa. Dariyar bakin ciki ta saki tana mai kauda kanta "Kada ka wahalar da kanka ga fidda hawayen da bazasu taba daina zuba ba a rayuwata Haris. Banajin zan daina zubar hawaye. Banajin ina da sauran dama na jin dadi a rayuwata. Don haka kabar sharemin abokan rayuwata,na tabbata su kadai sukafi kusanci dani, banason suma a rabani dasu." Baby ta fadi cikin sheshek'a,ya sunkuyo yana duban fuskarta "Nayi maki alkawarin idan har ina raye BAZAN BARKI BA tasleem. Daga yau inaso ki bani damar kasancewa mai share maki su, idan ina raye Tasleem bazan k'ara barinki kiyi rayu...." Meke damunsa ne?! Ya tambayi kansa, me yake shirin cewa? Ya dauke kansa ganin yanda baby ta saki baki tana kallonsa. Ya Salam,ya fada yana mai juya kansa. Murmushi kawai tayi "Kanason jin karashen labarina? Ban matsa maka.." "Baki matsamin ba,cigaba don Allah." Ta watsa mishi kallo mai tarin ma'anoni wanda yaji shi har tsakar kansa kafin ta gyara zama ta d'ora a inda ta tsaya............ 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (41) "Haka na tattara kayana na hada da muhimman takardun makarantana da kuma hotunanmu da duk dai abunda nasan zai amfaneni ciki kuwa harda Atmcard dina. Mai taxi na samu bayan munyi cinikin inda zai kaini na shiga. Abu na farko da na soma yi shine,rubuta wasika na damk'awa maigadin gidansu Rilwan,nace ya bawa mahaifinsa a karshe nayi mishi sallama na hau taxi,muna cikin tafiya ina kuka,naji maganar mai taxi yana fadin"Kinga Hajiya idan babu damuwa ga wata can da alama itama tashar ta nufa ko zamu dauketa?" Bance kala ba duk da nasan shatarsa nayi ina da ikon cewa aa saidai tashin hankalin dake gabana yafi gaban na bata lokacina anan. Ya tsaya ko kallon matar banyi ba,illai kuwa itama tashar dikkon ta nufa. Tana zama wani kamshi ya dokarmin hancina,duk da haka dai ban kalleta ba saidai na share hawayena sai numfarfashi nakeyi. "Sannu ko? Nagode fa." Tace dani, na dan kalleta,tabbas da ganin shigarta kasan tana hutawa kuma tafi kama da irin masu kud'in nan. Sanye take da wata atamfa yar ubansu tasha kwalliya ko yatsunta ka kalla kaga jerun zobbuna biyu na gwal sun wadatar dakai ka gane ba karamar Hajiya bace. Ita dinma ni take kallo fuskarta dauke da murmushi,wannan yasa na maida mata martani da murmushin da baikai zuci ba kafin na maida dubana ga gefen titi. Ina jinta tana waya kamar dai mota akayi niyyar aikomata don naji tana surfa ashariya tana fadin ita tafi karfin wulakanci,yasan yana. Tsoron matar tasa ya kwana da ita a hotel? Anan na fahimci lallai ba macen arziki bace. Har muka isa waya takeyi tun suna hayaniya har dai akarshe ta hau tuntsira dariya tana fadin babu komai ma zatabi motar kasuwa. Da isarmu na sauka,zan biya mai taxi ta dakatar dani tace ai nayi mata alfarma don haka kada na damu itama yimin zatayi,ina kallo ta biya. Nayi godiya,ina shirin kinkimar akwatina ta zagayo ta dubeni "Ina zaki ne?" Ganin da nayi mata na wacce ta fini shekaru yasa na amsa ba don naso ba don ta soma bani haushi ta soma takuramin. "Kano." Tayi dariya"Nima nan na nufa,tsaya a sama mana mota." Nidai bance uffan ba,abunda na soma tunani bai wuce ma ina zan nufa ba a Kanon? Waye zai amsheni da cikin shege?? Banyi mamaki sosai ba ganin Hajiyar nan ta dauki shatar karamar mota mai zuwa Kano guda daya. Tace nazo muje,wallahi Haris banji ko d'arr wai na rashin yarda da ita ba. Na sadakar idan ma yar yankar kai ce toh ta kaini a yankani na huta da bakar rayuwar da nake ciki. Koma dai menene alokacin ji nayi muje kawai. Motar mu ta d'aga daga ni sai Hajiyar nan da direba,lokacin wajejan uku na rana. Daidai lokacin da muka soma tafiya wayata ta dauki kara,shaf na mance ban kasheta ba. Na duba,sunan wanda na gani yasa a fusace na kashe wayar na fiddo sim din na cusa dukansu a jakata. Me kuma rilwan zai min? Ina waigowa karaf muka hada ido da Hajiyar nan. "Namiji ko?" Mamaki ya kamani,tayi murmushi tana kashe ido na yan duniya "Ai bakin cikin mace bai wuce akan d'a namiji baiwar Allah. Tun ganina dake a farko na fahimci kina cikin matsanancin damuwa,idanunki kadai zasu tabbatarwa mutum kinci kuka kin koshi. Idan bazaki damu ba,zaki amince dani ko zaki sanar dani matsalarki? Ni kuma zanyi maki taimako daidai gwagwadon iyawata." Na dubeta sai naji na aminta da ita. Hakanan na zayyane mata komai dangane dani da rayuwata. Ta jajinta min,na kara da cewa "Babu abunda na tsana a yanzu kamar cikin nan Hajiya! Ki taimakamin don Allah ki kaini inda kikasan za'a ciremin shi." Tayi murmushi ta rungumo kafadata "Kinzo wajen share hawayenki BABY." ***** Baby ta dubi Haris "Wannan itace Hajiya Hannatu Bariki wato MOMY. Itace ta sanyamin suna Baby wanda har ila yau ya bini, don wasu da yawa basu sanni da Tasleem. A gidanta na soma sauka inda kuma washegari ta kaini aka zubarmin da cikin jikina. Itace ta gogar dani a harkar bariki. Ita ta kasance tana nunamin hanyar da acewarta shi kadai ne jin dadin rayuwa babu wanda zai takura maka babu mai matsa maka. Tun ina tsoro har dai na bada kai bori ya hau,abun nufi dai ta shiga hadani da manyan alhazai wadanda cikin sa'a kowannensu rububina yakeyi. Komai Momi ita ta koyamin,Momi itace shugabarmu,yan mata da yawa da zauwarawa sanadinta suka rike kansu suka zama tantiran 'YAN BARIKI. Sai ya zamana nabar yayin dukkan manyan kayana,koda dai ba sosai daman nake sakasu ba nafi mu'amala da kananun. Saidai fa a lokacin ya k'aru sosai,Momi haka ta bada oda aka kawomin su kala kala daga Dubai. Haka nan babu kudina da ake tabawa,haka kawai jininmu ya hadu sosai da Momi tana ji dani kwarai da gaske. Duk da wasu kayan maye da Momi ke sha da sauran yan kungiya,bana shan komai sai taba,shima sai idan ina cikin matsanancin damuwa ko nishadi ban fiya sha sosai ba gaskiya." Baby ta murmusa adaidai nan,da alama kuma abunda zata fadi,fari ne fat a wajenta. "Daidai wannan lokacin ne,na shirya daukar fansa a wajen Usman. Ga Rilwan kuwa,Abbansa na zayyanewa komai a wasikar nan kuma inada tabbacin Abbansa mutum ne nagari da yasan ya kamata,kamar dai yadda nasan Rilwan da fadar gaskiya komai dacinta. Nasan bazai musa cewar shine yayimin wannan aika aikar ba. A yanda kuwa akayi na dauki fansar da taimakon Momi shine......." 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (42) Prince,dattijo ne mai kimanin shekaru arba'in,sunansa na gaskiya Alhaji Shitu Ibrahim. Shine na kusa kusa ga Momi,hakanan wani suka ne a gwamnati. Yana da yaransa ko kuma ince maka 'yan dabansa da yake sanyasu kashe dukkan wani rai dake kawomishi matsala a rayuwa. Daidai lokacin da muka sameshi da bukatarmu yayi dariya yace"Wannan abu ne mai sauki ai,yarana da suke kashe rai wannan karamin aiki ne a wajensu. Saidai kuma nima inaso a bani abunda na jima ina marari amma an tsaya yimin yanga." Ya karashe dadm dariyar 'yan duniya yana kallona. Murmushi nayi don a duniya ji nake alokacin ko me Prince ke so zan bashi saboda ya gama yimin komai da na bukata. Ba shiri na harhada kayana muka wuce dashi. Acan ya had'ani da babban yaronsa nayi mishi bayanin abunda nakeso ayi. Farko dai nayi mishi kwatancen inda babban shagon Usman yake domin alokacin yaci gaba har ma ya fito daga kwari ya bude babban shagon kaya wadanda yake sarowa daga Dubai. Nayi umarnin a k'onashi kafin nayi musu iznin nakastamin rayuwarshi ta hanyar yanke mishi dukkanin kafufuwansa." Baby ta dakata a yayin data tuntsire da dariya cike da jin wani irin nishad'i,Haris kuwa mamaki kwarai yakeyi ashe daman zata iya aikata mugunta har haka? Tunaninsa ya tsaya cak sa'ilin da dariyar dake kan fuskarta ta dauke ta koma zubar hawaye. Kanta ta girgiza cike da takaici "Saidai Haris, nasan ban dauki fansa ba. Domin babu yanda za'ayi na dawo da budurcina kuma mutuncina. Ya rigaya ya cuceni ya cuci rayuwata tun farko." Baby ta fada kafin ta kara duban Haris "Yanda kuwa na lissafa musu babu ko tangard'a hakan suka aikatamin. Ita kuwa Raliya itama saida suka tabbatar da fitowarta ita d'aya tana driving wataran suka tareta suka daure baki da idanunta. Ba wani abu sukayi mata mai yawa ba illah dai jibgarta dana sanya sukayi,yayinda a karshe dayansu ya kusanceta. Kafin su yi mota biyu da daddare daya yana jan nata,sauran kuma duk suna motar baya, wajejan sha biyun dare kenan. Daidai kofar gidan ya dire ta kafin ya koma motarsu suyi gaba ban kara bi takansu ba. Koda suka sanarmin sun cikamin aikina sai naji kuma na fashe da kuka kafin na saki dariya. Momy taso shima Abba a dan tab'ashi saidai naji bazan iya ba." Baby ta dubi haris cikin hawaye tace "Ban dauki fansa ba Haris,ban dauka ba. Saidai bana nadama ko kadan akan abunda nasa aka aikata musu a rayuwa. Haris tafiyata taci gaba kafin na samu na sayi gida wanda anan nake da zama yanzu. A hanya ne kuma na tab'a buge Manal da kullin kayanta,bayan na kaita asibiti naji likitan yana sanarmin wai tayi b'arin juna biyu. Koda ta farfado take bani labarin cewa marainiya ce,marikinta yayi mata ciki. Kaji silar haduwarmu da Manal. Dalal da Hibba a club muka hadu dasu, anan kuma kawancennu ya d'ore kafin daga baya nace subar gidan hayar da suke zaune su dawo nawa. Ni na hadasu da Momy,kaji yanda alakarmu tayi tafiya. Wannan shine labarina Haris." Haris ya numfasa kafin yace "Kin tafka kura kurai da yawa a rayuwarki Tasleem,ciki kuwa babban shine fitowa da kikayi kika fada harkar bariki maimakon ki kame kanki da mutuncinki,a'a saima zuciya data kwasheki kika maida kanki karuwar gaske. Kinyi ganganci kin manta da dokokin addininki daya hanemu aikata zina. Kuskurenki na gaba kuma,daukar fansa da kikayi akan wadannan bayin Allah inda kika manta cewar Allah baya kyale wadanda suka zalunci bawanSa,kika manta da kalmar hakuri har kika ji a zuciyarki cewar lallai ke da kanki kin isa sakawa kanki batare da kinyi hakurin ganin Sakayyar Ubangijinki ba. Rayuwar da kikeyi Tasleem,rayuwa ce ta wofi wanda karshensa nadama. Na hakikance ba kwadayin abun duniya ne ya kawoki bariki ba illah kawai kuncin rayuwa. Haba Tasleem,a rayuwa akwai wadanda suka fiki shiga kunci da wahalar rayuwa. Ki godewa Allah ma a gefe kina da iyayenki da yan uwa, wasu fa basu da ko daya,wasu rayuwarsu har su mutu cikin kunci da bakin ciki sukayita amma basu fada karuwanci ba,basu nemi daukar fansa ba illah dai sun kasance masu tawakkali da mik'a zuciyoyinsu ga Allah." Baby babu alamar jin haushin Haris a fuskarta saima kallo da take binsa dashi tana murmushi kafin daga bisani hawayenta su zubo. Ganin hawayen ya sanyashi tsayawa da maganarsa "Ina fatan ban b'ata ranki ba Tasleem?" Ta girgiza kai tana 'yar dariya "Wallahi baka b'atamin ba Haris. Asalima burgeni kayi,dadi nakeji a kasan zuciyata. Tunda na soma harkar barikanci,babu wanda ya taba yunkurin gayamin gaskiya saikai. Tun farko haduwarmu saida na fahimci kai din daban kake. Ban kara sakankancewa da lamuranka ba saida na hadu dakai a karo na biyu. Tabbas Haris kai mutumin kirki ne wannan ne yasa nayi mamakin yanda ustaz ya iya aminta da mutum irin Kb." Murmushi Haris yayi ya numfasa ya gyara zama kafin ya dubeta "Muna iya tafiya gaida Mamma?" Ta lumshe ido tana murmushi "Da gudu ma." Sukayi dariya kafin Haris ya mika mata ruwan roba daya siya zai sha "Oya,ga wannan sauka ki wanke fuskar nan taki, ki d'anyi kwalliyar nan taki bebinsu." Harararsa tayi a wasance,kafin ta narkar da fuska "Au ba taka bace?" Ya dubeta kafin ya basar da zancen ta hanyar fitowa ya bud'e b'angarenta ya amshi robar ruwan,yana kokarin budewa yace "Juyo ki wanke fuskarki." Ba musu ta gyara ta mika hannunta na hagu,yana zuba mata tana wankewa har fuskarnan tayi fayau,Baby ta gasken ta bayyana sannan ya zagayo ya bude boot ya dauko mata handbag dinta ya shigo motar kafin ya dire mata a cinya yana murmushi "Ayi make up please." Murmushin tayi kafin yayi addu'a ya daga gilasan ya kunna Ac,ya sanyamusu karatun al-kur'ani don kara nutsar da zuciyar Tasleem daga bisani yaja motar suka dauki hanyar Kazaure. Ita kuwa ta hau fente kyakkyawar fuskarta da kwalliya saidai bamai yawa ba. Bayan ta kammala ta dubeshi "Baka sanar dani abunda zai kaika garinmu ba?" Dam! Gaban Haris ya buga. Shaf ya mance da ainahin silar zuwansa Kazaure sai yanzu da Tasleem tayi tambayar. Ashe fa wai matar aure zaije zab'a. "Kayu shiru??" 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (42) Ya dan dubeta,ya rigaya ya gama tabbatarwa kansa cewar baby kyakkyawa ce ta gani a fada,tabbas baiga laifi ga KB dake makale mata ba domin kuwa idan zaka biyewa kyawun halitta da surarta,bakasan sadda zaka fada tarkonta ba. Yayi murmushi kafin yace "Garin iyayena ne." Ta fiddo ido kadan fuskarta ta washe "Haba? Ashe kaima dan garinmu ne? No wonder na ganka da kyau kamar aljani." Kallonta kawai yayi ya sakar mata murmushin da saida ta jishi har tsakar kanta. Tasan tun haduwarsu ta farko,tana jin wani al'amari bak'o game da Haris,saidai ita kanta tasan Haris yafi karfinta. Me zaiyi da 'YAR BARIKI? Ta maida kanta ta kwantar tana sauraron karatun Al-Kur'ani mai girma. Shi din ma kogin tunanin ya fad'a. Anya bai fada tarkon son 'YAR BARIKI ba? "A'a ban fada ba,just ina girmamata ne a matsayinta na wacce ke bukatar taimako. Ina kuma tausayawa rayuwarta." Ya fadi a ransa. ******* Hankalinsa a tashe,nutsuwa tak'i samun mazauni a kwakwalwarsa da jikinsa. Yana zaune sai afkin kiraye kirayen waya yake. Daga ya kira Manal,sai ya koma Dalal kafin a karshe yaji ta bakin Hibba. Momy ma ya kirata sau d'aya saidai ita kanta bata da labarin duniyar da Baby ta shiga. Zuciyarsa tayi bak'i har hasko Baby yakeyi kwance a kirjin wani da namijin. Kishi matsananci wanda har ya janyo sauyawar kalar kwayar idonsa. Tun tsawon daren jiya take lura da mijin nata, hakanan ko lokacin daya fidda kunya ko shayi yake waya a gabanta duk tana sauraronsa,hankalinta ya tashi jin cewar mace ce ta rikita Kabir har haka. Ta soma sharar kwallah saidai gogan baisan tana yi ba,kwata kwata ma baisan da wanzuwarta ba sai sambatu yakeyi a fili "Ina kikaje? Wane dan iskan kika samu har kika kashe wayoyinki Babyna?" Ire iren abunda yake fadi kenan. Maganarta ta katseshi "Wacece haka prince?" Ya dubeta,gaba daya baisan da ita ba a falon. Tsaki yaja ya mike ya dauki wayoyinsa zai shiga d'aki "Yanzu akan wata 'yar iska kake..." Fisgota da yayi ne a fusace ya sanya sauran maganar makalewa a fatar bakinta. Ya hau jijjigata cikin tsawa yace "Koda wasa kika kuskura kika k'ara kiran Babyna yar iska wallahi Yasmeen saikin raina kanki." Ta fisge jikinta tana hawaye itama a fusace tace "An fad'a d'in! Yar iska! Yar bariki..." Tass! Ya kwasheta da mari,kafin ya hankadata ta bugi bango ya nunota da yatsa "Wannan kadan kika gani! Wallahi akan Baby zan iya rabuwa dake Yasmeen! Sannan ki ajiye a ranki! Baby saita shigo gidan nan matsayin matata!" Ya kwashi wayoyinsa da suka tarwatse a k'asa yayi daki ya buga kofar a fusace. Yasmeen ta tsorata ainun,mikewa tayi ta nufi dakinta. Mayafinta da fos na kudadenta ta dauka,ta sab'i diyarta Nasreen dake bacci tayi waje. Ta rantse yau bazata kwana Abuja ba kuma ma a gidan mutum irin Kb. Maigadi yana tambayarta ko lafiya ta dakamishi tsawa "Budemin kawai!" Yayi mamaki don baisan Hajiyar tasu da haka ba,akwai ta da girmama na gaba da ita komin kankantar matsayinsa. Mace mai hankali da tunani,ga fara'a da hakuri. Ba musu ya bude a hanzarce ta sanya kai ta fita tana zubar hawaye. Yau kam sai KANO......! **** Karfe uku da mintuna na rana sai gasu a Kazaure. Gaba daya garin ya chanjawa Baby harma ta kasa sanin ta yanda zata soma kwatantawa Haris gidansu. Ga mamakinta taga yana ta shiga wurare bai tsaya ko'ina ba sai kofar gidan Liman. Tabbas gidan kakan nata ma yaso ya sauya mata sakamakon fenti da shukoki da aka k'ara mishi. Ta tsaya cak tana kallon tsohon dake zaune akan tabarma tare da makwaftansa suna hira,saidai suma hankalinsu ya dawo kan motar. Fitowar wata yarinya karama ce ta basu mamaki,tamkar an tsaga kara an karya ita da Baby saboda tsananin kamar da sukayi,tana wani yanga irin ta kananun yara masu iyayi ta isa ga tsoffinan ta zauna saman cinyar tsohon nan. Haris da Baby suka dubi juna,ganin hawaye a fuskar Baby da kuma murmushi yasa ya girgiza mata kai. Ta kwashesu da hannunta "Haris kayimin abunda har abada bazan mance dakai ba. Ka samu babban gurbi cikin zuciyata. Ina jinka sosai a jinin jikina kana yawo akowane sassa na jikina. Wallahi banajin zan taba mancewa da abunda kayimin. Nagode sosai." Yaji maganganunta har cikin k'ok'on ransa,ya kasa dauke idanunsa daga kanta. Ya rasa me yakeji game da ita,ji yakeyi tamkar kada su rabu. Inama zasu shekara a haka bayajin zai damu. Murmushin nan nata wanda yake tayar mishi da tsikar jiki ta k'ara yi mishi. "Fito muje,gaskiya ka bari ka huta saika karasa gida." Ya girgiza mata kai ya saki lallausan murmushi idanunsa a kanta "No,ki bari zan shigo anjima kinsan gobe fa zan tafi. Zanzo mu gaisa sai na kaiki ku gaisa da Kakannina." Ta marairaice fuska,kwalla ta ciko idonta "Gobe zaka tafi ka barni Haris?" Maganar ta shigeshi,yana kara jin zuciyarsa na shiga wani yanayi. Kwankwansa gilashin da akayi ne ya maido hankulansu ga wajen,Haris ya sauke gilas kasancewar gilasan daga wajenm akwai duhu. Dan saurayi ne,yana murmushi yace "Malam tambaya kukeyi ne?" Haris ya girgiza kai,baby ta sanya dariya "Baharu." Ta fada kafin ta fito,da gudu gudu ta isa ga Kakanta wanda da alama shi kam ya ganeta. Domin gaba daya ya mike yana farin cikin ganinta sosai,ta rungumeshi kafin kuma su zauna ta saki kukan farin ciki. Zuciyar Haris tayi babu dadi,ba abunda ya tsana sama da kukan nan. Dolensa ya bude motar ya fito suka gaisa da wanda ta kira da Baharu.....! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (44) "Tasleem,kukan na menene kuma? Me ya samu hannun naki?" Ta share fuskarta ganin yanayin Haris shima kamar baiji dadin ganin hawayen nata ba,ta dubi hannun kafin tace "Buguwa ce nayi Malam,amma yanzu da sauki sosai ma." Tsohon ya kurawa Haris ido da murmushi wanda haka halittarsa take,da wuya kaga gushewarsa akan fuskarsa. "Yaro kana yimin yanayi da aminina Hussein." Furucin Malam yasa Baby zubawa Haris ido kasancewar tasan Baffa Hussein sosai jefi jefi takan lek'a gidansu a baya idan tazo domin har baffa Hussein ya santa yana nuna kauna agareta har takanyi mamakin irin soyayya da shakuwar dake tsakanin wadannan bayin Allah biyu. Haris cikin murmushi yace "Lallai ma tsohon nan,tabbas idan na koma zan fadawa Baffa ka mance da autan jikansa,Haris." Mamaki karara ya sauka akan fuskar Baby hade da dariyar nan nata mai burgewa,haris ya daga mata gira yana murmushi. Malam kuwa hakora ya washe ya rungumo kafadar Haris yana dariya sauran tsoffi uku suna tayashi. "Allahu,daman kaine Harisu? Haka ka girma? Lallai Harisu baku da zumunci,da ace kun yo halin iyayenku da ba haka ba. Ina d'an wajen dan auta?(Alhaji idris)" "Yana can Abuja da zama. Kayi hakuri dan tsoho ba rashin zumunci bane,ayyuka suke rikemu acan." Malam ya jinjina kai,baby kam murmushi takeyi,yayinda ta kasa dauke fararen idanunta akan kyakkyawar fuskar Haris wanda samun namijin daya hada komai irinsa a fannin kyau na sura da halayya abune mai matukar wuya a zamanin nan. Ya kallota,tayi azamar mikewa tsaye tana basarwa da cewa "Bari naga kishiyoyina,don Allah dan tsoho kada ku bari yayana ya gudu tun yanzu,kunga fa ko abinci bamu ci ba." Haris ya hararota yana murmushi,tayi mishi gwalo kadan. Malam yayi dariya "Ai babu inda zai tafi yanzu,Baharu shigar da yayan naka dakinku yayi alwala yazo muyi sallah sai yaci abinci ko?" Suka mike,tuni Baby tayi gaba tana fadin zata turo yaro ya shigar mata da akwatin kayanta. ***** Tun a hanyarta take ta kiran wayoyin yayan nata amma yana ringing bai dauka ba. Taci kuka har ta koshi,ganin baya kusa yasa tayimishi dogon text inda ta gutsura mishi halin da suke ciki da KB da kuma tahowarta Kano da tayi. Daga karshe ta kashe wayarta gaba daya. Yasmeen kenan!! ***** Murna da hira ta karade bayan tsakanin mutanen gidan bayan da Baby tayi wanka da sallah. Tana sanye da doguwar rigar kanti. Alokacin tana zaune tana cin abinci anata hira. Makwafta sai shigowa sukeyi,Gwaggo Hajara ma nan tazo da kwanonta. Kowa yaga bandejin hannun Baby sai ya tanka,tana rufesu da fadin buguwa ce tayi. Wayoyinta kuwa har lokacin a kashe suke ta jonasu a chaji. Sallamar da akayi ta maido hankulansu,Haris ne a gaba sai Yaya musty a baya. Ganin Yaya musty yasa Baby sakin ihu ta mike ta rukunkumeshi suna dariyar farin cikin ganin juna. Gaban Haris ya shiga dukan uku uku,haka kawai ya tsinci kansa da jin haushin wannan rungumar da Baby ta yiwa wani. "Yaya mustyna,ashe da rabon rai ya k'ara ganin rai tsakaninmu?" Sai kuma ta soma hawayen farin ciki. "Yaya mustyna??" Ya maimaita a zuciyarsa,ashe har yanzu Yasmeen bata mance dashi ba? Har lokacin hannuwansu harde cikin juna,Haris ya kauda kansa ya wucesu zuwa ga mutanen gidan suna gaisawa. Kasancewar gwaggo Hajara ta samu labarin kowanene a wajen Baharu wanda yakai mata tsegumin zuwan Tasleem yasa ta ganar dasu. Nan fa murna ta k'aru,suka shiga tambayarsa mutanen Kano yana amsawa. A karshe yayi musu sallama bayan ya dire musu rafar kudi 'yan dari dari guda biyu ya mike suna fadin ya barshi amma da azama ya nufi waje. Ganin haka tasleem tabar hirar bayan rabuwa da Musty tabi bayansa a da sauri. Ganin yana shirin wuce zaurensu ne yasa tayi azamar riko hannunsa wannan yasa shi juyowa ya watsa mata kallon da yayi kama dana farkon ganinta dashi. Ta saki hannun dayake kanta a waye yake ta nuna kamar bata gane yanayin fuskarsa ba ta hanyar marairaicewa da langabar da kanta "Yanzu tafiya zakayi shine babu ko sallama?" Ya dan tabe baki yana mai zura hannunsa cikin aljihun wandon jeans dinsa,ya daga kafada "Gani nayi kina hira da yan uwanki banson katseki ne." Murmushi tayi kawai,ta soma fahimtar wani abu kadan akan fuskar Haris, mai yiwuwa yana dauke da ciwon da itama take dauke dashi. Ya katse tunaninta "Zan wuce." Ga mamakinsa yaga ta durkusa har k'asa tana dubanshi "Har na rasa manyan kalmomin da zanyi amfani dasu kuma wajen yin godiya agareka yayana,kayi jihadi babba wajen ceto rayuwata daga halaka. Daga yau na baka matsayi babba gareni. Zuwa yanzu bani da wanda yafimin.." Ya katseta shima ta hanyar yin durkuson a gabanta,yana kafeta da wannan idanuwan nasa masu kara fama mata ciwon dake ranta. Saidai ita kanta tana raina kanta a gaban Haris,duk wani haduwarta ganinta takeyi tsumma a gabansa. Ita kanta ta riga tasan Babban Goro sai magogin karfe,me namiji irinsa zaiyi da 'YAR BARIKI? Ta kauda kanta daga dubansa ganin bashi da niyyar kauda nasa akanta. Wai daman akwai abunda take ko kuma zata tabajin kunya acikin mutane? Bata taba kawowa ba kuwa ko a kanta,ya katseta a karo na biyu ta hanyar mikewa "Tashi Tasleem." Ta mike tsaye,bai kara dubanta ba yace "Kina iya rubutamin lambar wayarki,watakil na leko gobe kafin na wuce." Har ya soma tafiya sai kuma ya juyo dauke da murmushi saman fuskarsa wanda bata taba ganin irinsa ba a tattarr dashi. "Sannan ki sani,matsayin kanwata kike Tasleem. Bana bukatar ki yawaita godiya gareni. Ki cigaba da godewa Ubangijinki. Hakanan ya dace kiyi istibra'i. Sai Allah Ya kaddara saduwarmu Tasleem." Ya soma tafiya da baya da baya, hawaye taji sun taho mata yayinda ya juya ya fita da sauri saurinsa. Ta tsaya cak tana binshi da kallo zuwa lokacin hawaye sun sauka saman fuskarta. A gaban idanunta yaja motarsa bai k'ara ko kallon kofar gidan nasu ba. "Small." Taji muryar Yaya Musty ya fadi ta bayanta,wannan ya fargar da ita a inda take tsaye. 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (45) Ta dubeshi tana murmushi,yayinda damuwa ta sauka saman fuskarsa shi kuma. "Kin tsaya anan? Ko bakiso ya tafi bane?" Abunka da wacce bata iya boye damuwarta ba tace "Banso ba,ya tafi ya barni da damuwa marar misaltuwa saidai yace watakil kafin ya wuce ya biyomin muyi sallama." Musty ya k'ura mata ido yana kallon kwayar idanunta. Akwai wani kwantaccen sirri game da Haris a cikinsu. "Kanwata are you in love?" Tayi tsai domin batayi mamakin jin wannan tambayar ba,inda takeson Yaya mustin nata kenan,nan da nan ya dago damuwarta ko wace iri ce. Ta basar ta hanyar dariya ta soma tafiya tana fadin "Yaya mustyna kenan,ina Haris ina mace irina?" Ya riko hannunta wanda yayi silar tsayuwarta,ya jawota baya kadan yana dubanta da idanunsa da suka bayyana bacin rai da damuwa karara a cikinsu,mamaki ya hana baby magana sai ya rigata da cewa "Ya kike irin wannan maganar sisna,wa zaik'i mace kamarki? Ko kina da wani aibu ne?" Ya karashe bayan ya saketa yana murmushi a sanyaye,bata yardarwa kanta hakan yayi niyyar fada ba sakamakon zafin da ya nuna a farko. Batace komai ba banda murmushi da "Uhm" daga haka tayi ciki. Ya bita da kallo rai a bace,wai daman Tasleem ba sonshi takeyi ba kamar yanda ya jima yana yaudarar kansa? Yaya mustyna! Yaya mustyna! Me hakan ke nufi?!! Tsaki yaja bazai kuma iya komawa cikin gidan ba kawai sai yayi gaba zuwa gidansa rai babu dadi domin ya gama lura Haris ya samu gurbi a zuciyarta. ***** Mutanen gidan sunyi farin cikin ganinsa sosai. Nan aka shiga hidima dashi,sai abinci ake ajiyewa agabansa. Hankalin Haris ko kusa baya kan yan matan da suka had'e cikin kwalliya sunata shawagi a falon wajen kawo mishi abinci,ya tabbata an riga an basu labarin abunda ya kawoshi. Sai hirarsu sukeyi da kakarsa,Hajja. Koda ya kammala mikewa yayi ya nufi sashen kishiyoyinta suka gaisa kafin ya nufi bangaren kakansa,Malam Hussein. Nan ma suna hira yake sanar dashi tare sukazo da Tasleem diyar gwaggo maryama 'yar amininsa Liman. Ai sai Malam Hussein ya tashi zaune fuskarsa a sake sosai. "Jikar Abdulmalik ce? Ikon Allah,daman kunsan juna ne acan Kano?" Haris ya rasa amsar da zai bashi a karshe yace "Eh munsan juna,tare mukayi makaranta saidai banma san 'yar gwaggo maryama bace saida muka hadu itama zata zo nan take bani labari." Kakan nasa yayi dariya,cike da mamaki yace "Wai kuwa d'an tsoho wane irin aminta ke tsakaninka da Liman? Na lura kuna kaunar junanku fiye da tsammani." Jin tambayar ya k'ara sanya Malam dariyar farin ciki "Bazaka gane ba Harisu,kaunar da muke yiwa junanmu ta samo asali tun daga iyayenmu da suka rasu,saboda karfin zumuncin ne,yasa mahaifina sanyamin sunan mahaifin liman din,wato Hussein yayinda shima yaci sunan nawa mahaifin Abdulmalik. Bayan haka,Allah Ya riga ya sanya mana kaunar junanmu fin tsammani Harisu. Wanda muke burin wataran mu kulla zumuncin da zai d'orar. Saidai kasan a zamanin nan ba'a yiwa yara dole,amma har gobe bamu bar burin wasu cikin jikokinmu ba su share mana wannan hawayen." Haris yayi murmushi,baffa ya katse tunaninsa "Ina fatan kayi abunda akace ya kawoka?" Haris ya hade fuska "Na rasa wacce zan zab'a domin na lura jikokin naka akwai yanga. Duk kama sukeyimin da juna ma." Sukayi dariya,Baffa yace "Ja'iri,ko kanawan dabo ba zasu nunawa mutanen Kazaure kyawawan yan mata ba shiyasa har zuwa yau ka kasa zab'en matar aure. Kada ka damu ka nutsu ka zab'a bazan bari Aliyu yayi maka dole ba." Daga haka suka tab'a hirarsu ta zumunci kafin Haris yayi mishi sallama ya fice zuwa d'akinsa. Hankalinsa yakai ga wayoyinsa wanda ya barsu suna chaji,ya dauko yana dubawa. Missedcalls har fin goma,shida kuwa na kanwarsa ne. Yayinda daya na Abba sai kuma daddy daya kira sau uku. Hankalinsa yafi raja'a ga na kanwarsa. Yana shirin kira ya hangi sak'onta. Tun soma karantawarsa ransa yayi mummunan b'aci,jikinsa har rawa yakeyi. Wai Kb wane irin d'an akuya ne? Meyasa baya shakkar b'ata ran mutane? Ya lalubi layin Yasmeen ta daga tana kuka alokacin tana kwance a gadon mami(Maman kb wacce ta gama fusata). Cikin kuka tace "Yayana kaga text dina? Yayana ka ceci rayuwata bazan iya yinta ba saida Kabir. Na shiga uku." Ya runtse ido yanajin bakin ciki har ransa "Wacece yarinyar?" Shine kawai abunda ya nemi sani. "Baby yake yawan ambato." Tuni idanun Haris suka bud'e,Baby?!! Akanta Kb yake cin zarafin kanwarsa? Kawai sai ya kashe wayar a fili ya furta "Na rantse da Allah Kabir bazaka tab'a aurar Tasleem ba. Daga kai har ita zan nuna maku ni Haris na isa." A fusace yasa kai,bai zarce ko'ina sai d'akin BAFFA......! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (46) "Ya wajen yayan naki? Ai farko mun damu da rashin samunki a waya. Wancan zuwan da sukayi na karshe yace min kin koma makaranta da zama anan Kano kuma ya hanaki yawan amfani da waya a dalilinsa nason ganin kin mayarda hankali ga karatu, har ina fad'a ina cewa me zaisa a wannan zamanin baligar mace tabar gaban mahaifanta ta koma jami'a da zama. Haba Tasleem,shi Khalid(Abba waziri,mahaifinta) din baiga kuskuren yin hakan ma? Koda dai na yarda da tarbiyyar da kika samu wajen maryamu amma hankalina bai kwanta ba Tasleem,nafison ganinki a d'akin mijinki." Baby dake sauraron dogon bayanin kakarta,a gefe idanunta yana kan wannan 'yar budurwar mai matukar kama da ita tunaninta kuwa ya raja'a akan zuk'i tamallen da Yaya Abdullah ya shararo ya gaya musu. Kenan cewa yayi tana makaranta? Ikon Allah kenan. Ta numfasa ta kauda maganar "A ko'ina Allah kan tsare bayinSa inna,kubar damuwa. Wai wacece wannan duplicate din tawa?" Inna ta dubi yarinyar duk da bata gane turancin ba saidai ta fahimci baby bata ganeta ba. "Lallai ma 'yar nan,keda har aike kikayi na sutura a kawowa kanwar taki tana jaririya? Aisha humaira ce fa,taci sunan aminiyar uwar taki. Lallai baki kyauta ba tasleem." Tasleem idonta ya cika da kwalla,inna ta katseta da cewa "Ai kusan sa'annine da takwararki,ko wannan zuwan nasu na karshe karkiso kiga har tasleem karama ta kusa kamota a tsayi." "Wacece mai sunana?" Anan kuma inna ta tsaya cak tana dubanta,wannan karon mamakinta da shakku sunfi na koyaushe domin kuwa tun zuwan Tasleem take lura da yanda ta chanja duk da tasan yanga da nuna aji halinta ne saidai zuwa yanzu ta soma zargin kodai Tasleem bata wani zumunci da yayan nata. "Kinga abunda yasa banason makarantar kwana ko? Kada dai kicemin bayan mu da kika daina zumunci damu,yayan naki ma bakya zuwar mishi hutu kamar yanda ya fadamana ne? Nayi mamakin jin cewar kin manta da d'iyarsa." Sai lokacin Baby ta farga da kuskurenta,ta wayance ta hanyar dariya duk da har lokacin tana fushi da yayan nata hakan baisa ta karyatashi ba. "Kai inna,karatu fa yayi zafi duka duka munkai wata bamu hadu ba,inada matsalar yawan mantuwa ni ki gayawa liman ma ya nemar mini maganinsa." Inna tace "Assha,naga alamun hakan kuwa. Tabbas dole ki nemi magani da kuruciyarki da komai wannan cuta ce babba. Saiki bar yin fitsari a inda kike wanka,domin shima yakan jawo larurar yawan mantuwa. Zan kuwa gayamishi." Tasleem ta janyo hannun humaira wacce ta kammala cin tuwon dare,ta rungumeta kafin ta sumbaci goshinta. "Ni yayarki ce, kina sona?" Humaira tana dariya tace "Eh." Ta kara rungumeta tana kokarin danne hawayenta,burinta gari ya waye taje ga mahaifiyarta. Daren bata iya bacci ba,sai kuka da taci k'asa k'asa tunanowa da gurb'atacciyar rayuwar datayi a baya, gashi tana kunyar yan uwanta su samu labarin. Batasan yayanta yana mugun sonta ba sai a lokacin,tunda har ya iya sanyawa 'yarsa sunanta ayanzu kam bata da burin daya wuce ta sanya yarinyar a idonta. Har zuwa lokacin bata da niyyar bud'e wayarta domin batason amsa wayar mutanenta agaban mutan gidan. ****** Baffa ya dubeshi ya ajiye littafin karatunsa "Lafiyarka kuwa Harisu?" Harisu ya zauna kansa a kasa "NA SAMU MATAR AURE BAFFA.....!" "Alhamdulillah! Wacece?" Ya gyara zama har lokacin ransa a matukar b'ace yake..... 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (47) Yayi kokari sosai wajen danne mugun tsanarta dake taso mishi aduk sadda ya tuna cewar ita ke haddasa rashin zaman lafiya a gidan kanwarsa. "TASLEEM." Ya karashe cikin d'acin zuciya,yayinda idanunsa suka kara kad'awa. Ji yayi Baffan ya rungumoshi cikin matsanancin farin ciki wanda sanin amintar bayin Allahn a yanzu yasa ko kusa baiyi wani mamaki ba yanzun. "Allah Ya albarkaceka a gaba daya rayuwarka Harisu,kamar kasan addu'ar dana gama yi kenan akan Allah Yasa kace kanason jikar aminina. Allah Yayi ni Husseini ban mutu ba zanga aure ya kullu tsakanin zuri'ata dana Abdulmalik? Allah na gode maKa daka amsamin addu'ata nan take. Saidai kuma harisu bazan baka auren jikata ba har sai ta amince zata aureka don haka ka tashi ka tafi zuwa gobe sai na tuntub'eta. Allah Ya tashemu lafiya." Haris ya mike jiki babu kwari ya fice zuwa d'akin da aka tanadar masa. Kwanciya yayi akan makekan katifar sakamakon kansa da yaji yana sarawa. Anya bai kwari kansa ba kuwa?!! No! Bazai yiwu kuma yabar rayuwar Yasmeem cikin garari ba. Tabbas rayuwarta da farin cikinta sun dogara ne da Kb,burinta a duniya bai wuce Kb ba. A yau aka wayi gari Kb ya auri Tasleem,wulakanci da bakin ciki sune abunda zai biyo bayan auren ga Yasmeen. Shikam ya gwammace yayi wannan jihadin,alhalin ma a yanzu koda kud'i yana da yak'inin Baby bazata k'ara waiwayar karuwanci ba. Yana jin tsanarta a wani sashen zuciyarsa yayinda wani sashen kuma yakejin sassauci game da ita. Ya rantse sai ya rabata da Kb hanyar data dace,kb bai isa ya nemeta ba idan ta zama matarsa. Bai isa koda wasa ma ya tunkareta ba,ba wai don kishinta yakeyi ba(a fad'arsa kenan!!),sai don samawa kanwarsa 'yanci da kuma farin cikin gidan aure. Wanda bazai tabbata ba sai yayi nasarar raba wad'annan shaid'anun biyu..! ***** Da sassafe ya kammala komai ko karyawa baiyi ba ya fito da shirinsa na komawa garin Kano domin bashi da bukatar k'ara yin tozali da Baby hakazalika hankalinsa ya tafi gaba d'aya ga kanwartasa. Ya shiga ya samu Baffansa yana lazumi,ganinsa cikin shiri yasa Baffa watso mishi tambaya "Harisu tafiyar ce?" Haris ya danyi murmushi kai da ganin idanunsa kasan bai samu wadataccen bacci ba "Tafiyarce Baffa,akwai ayyuka masu yawa da zanyi a yau in sha Allah." "Toh madallah,game da zancen da kazo dashi kuma fa?" Yaji ransa ya b'aci tunawa da batun aurensa da Baby wanda ya k'ak'abawa kansa, "Baffa na baku nan da karshen sati,duk abunda kuka yanke in sha Allah zan dawo sai naji." Ya jinjina kansa "Ai shikenan,lallai kuma ka gayawa iyayenka maza ina bukatar ganinsu idan zaku dawo ku dawo tare. Allah Ya tsare hanya. Ka shiga kuyi sallama da aminin nawa ko?" "Amin." Daga haka Haris ya fice batare da yayi na'am da zancen baffa na karshe ba,bayan ya yiwa mutan gidan sallama ya fita,yan matan da bai zab'a ba kenan! Yana sane ya share batun zuwa gidan liman,ya tayar da motarsa wacce tun jiya da yamma yasa aka wanke mishi tayi k'al. Ya zauna kenan yana kokarin daura seat belt ya hango wata sark'a a k'asan mazaunin kusa da direba. Hannu yasa ya dauka,ba shakka sark'a ce da baby ke ado da ita a k'afarta. Zuciyarsa ta d'an sosu,ji yayi kuma yana kewar rashin abokiyar hira a kusa dashi. Saidai tunawa da yayi da kanwarsa da halin da take ciki yasa yayi azamar ajiye sark'ar a saman kujera ya kunna karatun kur'ani mai girma yayi ribas ya d'auki hanya...sai Kanon Dabo.....! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (49) "Ya akayi Kabir?" Ya lumshe ido ya sauke ajiyar zuciya cikin jin dadin muryar daya jima yana kewarta. "Idan da abunda yafi tashin hankali da matsanancin damuwa tsanani,toh kin sanyani a ciki Babyna. Nayi mugun kewarki har na zama tamkar zararre wanda hakan ke nema ta shafi mu'amalata da kowa da kuma aikina. Where have you been for so long? Kinsan irin halin da na shiga?" Ta numfasa cike da takaicinsa,ita kam yanzu haushi ma yake bata,ta dan ja karamin tsaki "Banson takura ne Kabir,na d'anyi tafiya bana zaton dawowata nan kusa ma." "What?!!" Ya fad'a da k'arfi yana mikewa zaune daga kishingid'ar da yayi a daya daga cikin kujerun na babban airport dake birnin tarayyar Abuja,alokacin yana shirin zuwa Kano ne domin amsa kiran iyayensa duk akan matar da sai daga baya ya gane rashin kyautatawarsa gareta. Yayi kokarin saita kansa ganin yanda mutanen wajen suka zubomishi ido gaba daya. Cikin tattausar murya yace "Meyasa kikeson tayarmin da hankali babyna? Jikina ya bani kina tare da wani shegen shiyasa kika chanjamin. Wai me yake baki? Me kuma yake maki da bana iya kokarina wajen yi maki?" Hawaye suka surnano daga idanuwan Baby,ba wai na wani abu bane sai jin tsanar kanta da kanta. Wai har itace yau ake gayawa haka? Karuwa ta gaske ake daukarta. A fusace tace "Nabar wannan rayuwar kabir! Bana tunanin daga yau zaka kara ganina ballantana akai ga kaji muryata! Bakai ba,kowanene nabarshi har abada na gane wannan rayuwar ba rayuwa ce..." Dariyar daya sanya kamar wani zautacce yasa Baby tsayawa cak, hakazalika mutanen dake zaune tare dashi suka zubamishi ido domin zuwa lokacin baiko damu dasu ba. "Karya kikeyi?! You can never live without me baby! Ke d'in tawa ce, baki isa kiyimin YANKAR KAUNA ba! Dani dake babu mai rabamu,kuma ki sani, ina nan ina jiranki. Ki ajiye a ranki baki da miji sai ni! Saina aureki kota halin k'ak'a sai na cigaba da gabatar da rayuwa dake!" Ta katse wayar gaba daya a fusace ta fiddo sim ta tauneshi ta furzar. Kawai sai ta durkushe ta fashe da kuka. "Adda menene?" Maganar Humaira ya ankarar da ita a inda suke, ta share hawayenta ta mike tana kokarun kakalo murmurshi "Bakomai kanwata,muje." Tafiya takeyi saidai komai na kalaman kabir yana dawo mata,taji ta tsani kanta. Inama za'a maido hannun agogo baya,inama inama zai zamana wannan kaddarar zata shafe a tarihin rayuwarta. Kai inama ace Abbanta bai auri Raliya ba har ma hakan yayi sanadin fad'awarsu ha'ula'i. Haka tayi ta tunane tunane jikinta babu laka har suka iso gidan auren Mamma. Baki ta saki ganin makeken gidan wanda bata taba zaton anan Kazaure za'a samu gida mai kyawun fasali kamar na turawa ba. Humaira ta katseta tana jan hannunta "Nan ne gidan fa Adda." Wata yarinya suka soma cin karo da ita tasha d'amara,ta cika eyeshadow a saman idonta,ga kuma jan baki data maka. Lukuta ce ta gaske,tana tsallenta kamar ba budurwa ba tana b'alla rake. Ganinsu yasa tayi d'if tana bazo ido. Kafin ta washe baki ganin Humaira ":Yar Humeme,wacece wannan kamar baturiya?" Baby murmushi kawai takeyi ganin yarinyar,kamar dai tana da matsalar yarinta amma irin wannan kwalliyar ai an bar yayinsu. "Addana ce, daga birni." Yarinyar ta cuno baki. Wani saurayi mai shekaru sha takwas ya iso wajensu yace "Kedai kam Safiya bazaki bar shiririta ba,inace anti tace ki tafi gidanku kibar fitowa idan kaka tana bacci? Wannan yar birni ce,kinga ma yanda ake kwalliya ba irin naki ba." Ya karashe suna dariya har baby wacce abun ya bata dariya,wacce aka kira da Safiya ta murguda baki ta k'ara b'antalar rake "Oho dai,Ali nuhu ma kansa yace mata suna kauye." "Yauwa d'an k'arasa mana." Ta harareshi tayi gaba tana tsalle tsallenta tace "Akwai wanka." Ta fice, saurayin ya dubi baby sukayi dariya. Ya dan russuna ya gaisheta gami da tambayar wanda take nema. Kafin ta bashi amsa humaira ta cafe "Yaya Nura,addana ce ta Kano." Ya kalli humaira ya kalleta,tabbaa yaga kama ya kara washe baki "Yaya tasleem,right?" Ta lumshe ido hadi da jinjina mishi kai lokaci daya. Ai sai ya sheka da gudu "Kai ka kai,amma yau ni zan soma kaiwa antinmu albishir." Jin haka Humaira ma tabi bayansa a guje. Dariya baby tayi ta mara musu baya tana mai zumudin yin tozali da mahaifiyarta.... ****** Haris cike da mamaki ya dubi Yasmeen bayan sun keb'e a farfajiyar gidan inda tayo mishi rakiya zai koma ofis lokacin karfe ukun rana. "Ashe kina da hankali har haka little? Kwarai banyi tsammanin zaki iya b'oyewa iyayenmu ainahin abunda ya had'aku da KB ba." Yasmeen tayi murmushi mai ciwo "Bari kawai yayana,wallahi inason Yaya kabir kai kanka shaida ne. Gani nayi a yanda kawai Daddy ya dauki zafi jin cewar yace na dawo ba tare da wani dalili ba(kamar yanda ta fad'a musu kenan don kare mijinta),kar kaso kaga yanda ya fusata sai faman bud'e wuta yakeyi. Ya kake tunanin idan sunji har marina yayi akan karuwarsa? Ba yanda za'ayi nayi gangancin da za'a rabani dashi. Kaima ina rok'onka don Allah kada ka nunamishi kasan zancen." Ya kara tsintar kansa da kauna da matsanancin tausayin kanwar tasa, shi kuwa ya za'ayi yayi gangancin barin Tasleem ta ruguza farincikinta? Bazai yiwu ba. Ya numfasa "Baki da matsala dani little,saidai ina rok'onki da ki rage son d'a namiji har haka kada ya zame maki babbar matsala fiye da yanzu. Ki cigaba da addu'a Allah Yayi mana magani. Bari na tafi, Abba yana jirana." Ta tareshi "Af,baka sanarmin wacce ka zab'o mana matsayin antin tawa ba? Kodai zatona ya zama gaskiya,Zahra ce?" Yayi murmushin dole "No.. Baki canka ba." Ta dan nuna damuwarta,ganin ta bude baki zata k'ara magana ya bude motarsa ya fad'a "Ke kyaleni kinji ko? Sai mun dawo da yamma." Daga haka ya fice, taso taji kowace mai sa'ar ce tayi nasarar samun namiji irin Haris? Da ace KB yana da kyawawan halaye irin na Haris da ta bugi kirji ta kira kanta mai sa'a. Saidai abun takaici ya zamana bashi da hali..... 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (48) Fuskarta ta bayyana tsananin damuwa da mamakin jin cewar wai Haris da take zaman jira su karb'i lambar juna ya koma Kano. Menene haka Haris yayi mata kodai mantuwa ce yayi? Inna dake lura da ita tace "Kin shirya zuwa gaida malam husseini daga can ki wuce gidan mahaifiyarki,kuma kin cire mayafi kinyi zaman dirshan daga samun labarin tafiyar Harisu. Kina nufin bazaki ba saboda shi?" Baby ta kalli kanwarta humaira wacce duk ta shanye janbakin data shafa mata a lebba kafin a sanyaye kuma ta janyo mayafi wadatacce wanda ta dauka cikin kayan mamma data barsu a dakin. "Banji dadi bane daya wuce batare da munyi sallama dashi ba. Amma ba hakan na nufin bazanje ba. Taso muje Humaira." Ta dauki wayoyinta fuskarnan ta baby babu walwala ta zura takalminta mai tsini wanda sanyasu har sun zame mata jiki. Inna dai takalmin take kallo cike da mamaki kodayake ta lura duk takalma uku data zo dasu haka suke da tsinin dunduniya. Ta kasa dai hakuri ta tofa "Wai Tasleem baki tsoron wadannan takalman su karya maki k'afa?"(Kamar dai yanda kawata Ummu Abdool ta sanya ta fad'i cikin taron mutane koda yake farkon zuwanta birni ne👌) Baby tayi murmushi "Inna ai na rigaya na saba,inajin dadinsu sosai." Inna ta tabe baki "Oh,duk wannan tsawon naki neman k'ari kikeyi. Toh Allah Ya tsare,sai kun dawo." Ta amsa kafin ta fita rike da hannun Humaira wacce ta rigaya ta mamaye zuciyarta. Tayi mamakin samun Malam Hussein din tare da Liman a falonsa. Ashe ma yana gidan? Suna ganinta fara'arsu ta k'aru inda Liman yace "Ga jikar taka ai." Cike da ladabi ta gaishesu suka amsa,Malam Hussein ya sanya mata albarka kafin ta mike tayi musu sallama ta fita. Duk da hakan saida ta nufi gidan ko Allah zaisa ta hadu da wanda zai bata lambar Haris. ****** Alhaji Aliyu Hussein(mahaifin Haris, su shida iyayensu suka haifa. Shine d'a na farko namiji,sai mace mai bi masa ta rasu, sannan Kawu Usman,Kawu Bilal da autarsu Hajiya Barira dake aure a garin Maradi,jamhuriyar Nijar da kuma Hajiya Mariya(mami,mahaifiyar Kb) Gaba dayansu mazan idan an cire Abba dake kano,suna zaune ne anan gidan kowanne da bangarensa. Fa'iza,Habiba 'ya'ya mata ne ga Kawu Usman,manyan mazan su uku ne. Yasir,Abdulmalik(Babban yaya) da Faisal Rahina,Badiyya da Atika 'ya'ya matane ga Kawu Bilal,rahina tayi aure sauran Badiyya da atika wadanda sukayi candy. Bashi da d'a namiji. Sai kuma babbar diyar Hajiya barira ta fari kafin tayi aure na biyu ta koma Nijar da zama,Zahra. Wacce ke a hannun kakarsu uwargida kuma amaryar Malam husseini,Hajja Kubra. Kyawawan yan mata saidai na wata tafi na wata,hakan bai hanasu sakin baki wajen kallon wacce suka tabbatar ta ketaresu a komai ba,wacce kamshinta mai sanyi ya soma ziyartar hancinsu kafin kyakkyawar surarta ta bayyana a gabansu gami da zazzak'ar muryarta wacce tayi musu sallama da ita. Gaba daya kuwa yan matan sun had'u suna masu jimamin tafiyar Haris wanda bai zab'i d'ayansu ba. Kada ma Zahra taji labari,yarinya mai tsananin kunya da kawaici saidai a k'asan ranta ba k'aramin so take yiwa Haris ba. Abunda batasani ba,daman Haris a farko kafin yazo ya kudurtawa ransa matukar anyimishi dole ya fito da mata cikinsu toh hakika yafi ganin dacewar zab'ar Zahra. Ya lura akwai nutsuwa da tarbiyya tattare da ita duk da dai sauran ma akwai saidai basu da kawaici kamarta. Ko jiya da suke shawagin nan bai ganta ba saida yasa aka kirata suka gaisa. Wannan ba karamin dadi ya yiwa Hajja Kubra ba ganin matukar dacen data hanga tsakanin Haris da Zahra. Hakan yasa ta kudurta yiwa Malam zancen. Bayan gaisuwa ta sanar dasu itace tasleem. Zahra ta tareta da murmushi "Wow,kece d'iyar gwaggo maryama ta Kano ko? Duk sadda naje gidanta bamu da hira sai taki. Tabbas kinyi kama sosai da Humeme." Kasancewar haka take kiranta,sukayi dariya gaba daya. Bayan gama gaisuwarsu ta nemi gaisawa da Hajja Kubra,har cikin dakinta Zahra ta jagorance ta,itama ta nuna murnar ganin Tasleem a karshe sukayi sallama. Ta sanya Zahra yi mata rakiya sauran sashen kafin ta dubeta har lokacin tana murmushi haka kawai taji Zahra ta burgeta. "Nagode 'yar uwata,bari na karasa gidan Mamma." "Lah bazaki shiga gidan Malam Ibrahim ba?" Cikin rashin sani tace "Waye hakan?" Zahra tayi dariya "Mahaifin amininin Kawu Abba ne dake garin Kano. Kawu Abba kuma mahaifin Yaya Haris ne." Jin wannan bayanin,Tasleem ta jinjina kanta,ta hakikance gidan kakannin KB kenan. Gidan yana kallon juna dana kakannin Haris suka shiga. ***** Matansa biyu,Hajja Badi'atu da Hajja Atine. Yaransa tara cif. Hajja badi'atu tana da biyar yayinda Hajja Atine keda hudu. Alhaji Idris(Babangida),mahaifin Kb shine babba. Sai Safinatu, Aisha(mahaifiyar Haris),Bello,Abdulmalik(Baba karami). Ya'yan Hajja Badi'atu kenan. Matan duka suna gidan mazajensu. Mazan kuwa idan an cire Daddy suna nan agidan da matansu da yaransu. Hajja Atine kuwa,Garba,Fatima,Hafsa da Zakari. Suma duk sunyi aure sun hayayyafa. ****** Babu inda Zahra bata shigar da tasleem ba,a inda Tasleem ta rasa ma da wanda Kb ke kama tsakanin iyayensa. Idan ta hangi kamanninsa da Hajja badi'atu saita hango da Malam ibrahim. Karshe Tasleem ta yiwa Zahra godiya suka kama hanya da kanwarta wacce tayi wayon sanin gidan mahaifiyarta." Sai lokacin ta kunna wayarta,da kamar mintuna biyar kiran Kb ya shigo. Wannan yasa dole ta dakata a gefen wata bishiya domin amsa kiran nasa....! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (50) Hankalinsa idan yayi dubu ya tashi,Allah Allah yakeyi jirginsu ya tashi yaje ya nemi inda baby take ya dauketa koda ta halin k'ak'a ne. Shaf ya manta da dalilin zuwansa Kano akan matarsa ce,ana kiran masu tafiya Kano yayi zumbur ya mike yayi gaba. Baby tana neman rainamishi hankali,shi kam bayajin zai iya rabuwa da ita a yanzu. Ko me za'ayi saidai iyayensa su amince su aura masa ita koda na watanni ukun ne yanda kungiyarsu tace idan yaso daga baya zai san yanda zai fiddata cikin shaid'anin kungiyar nan. ****** Da gudu ta isa ga Mamma wacce ke tsaye tana sauraron maganar Nura da humaira duk bata gama yarda dasu ba. Jin tasleem a jikinta tana kuka yasa ta tsaya cak,itama hawayen ne suka cika idanunta. Sallamar dattijon ta katsesu,duk suka waiga suna amsawa. Yayi tsai ganin bakuwar fuska,kafin ya jefo tambaya,nura ya amsata "Adda tasleem ce fa Dad,'yar anti ta birni." Fara'arsa ta k'aru,fari fari ne da silkin bak'i,dogo ne yana da jiki. Ganin Mamma ta nufeshi gami da amsar ledar hannunsa a ladabce ya fahimtar da baby lallai shine mijin Mammanta. Murmushinta ya fad'ad'u itama had'e da hawayen farin cikin ganin irin sauyin da Allah ya yiwa mammanta. Tun kafin yakai ga k'araso kusa da ita ta zube gwuiwoyinta k'asa ta gaisheshi "Ina kwana Kawu." Ya mikar da ita ta hanyar riko hannunta yana 'yar dariya "Ashe bazaki bani matsayin uba ba tasleem? Toh ni kuma na daukeki matsayin d'iyata tun kafin na sakaki a kwayar idona. Kiyi kirana da Dad kema amma banjin dadin uncle dinnan." Mamaki ya kamata tana dariyar farin ciki,kawai saita fashe da kuka,ashe wataran zata samu wannan soyayya irinta uba? Alhamdulillah. Dad ya katseta ta hanyar duban Mamma fuskarsa ta cika da farin ciki "Yau duk abunda za'ayi a gidan nan na fannin girke girke da shaye shaye ya zamana yazo daidai da ra'ayin d'iyata kada ayi abunda bataso." Daga haka ya dubeni "Menene abun kuka my daughter? Sai kisa naji kamar bakyayin uban dani." Tayi azamar share hawayenta ta dubi mamma wacce murmushi kawai takeyi tana kallonta kafin ta maida dubanta ga Dad "Ba haka bane Dad,kukan murna nakeyi." Ya dafe kanta cikin murmushin yace "Ya isa hakanan kada yayi yawa kuma. Bari na shiga ciki." Ya mike ya nufi sama. Baby ta zauna saman kujera tana dariya tace "Mamma nayi maki murna." Ta harareta kadan,nura yaja hannun humaira yana fad'in "Yar kanwata zo mu amso alawa wajen Dad." Suka haye saman tare,Mamma da Baby suma saman suka nufa d'akin Mamma. Ta dubi hannun diyarta "Ya naga kamar hannun naki a kumbure?" Ta d'an dubi hannun,ashe fa dazu da zatayi wanka ta fidda bandage din,ta dan tabe baki kadan "Buguwa nayi kuma har yanzu yanamin zafi kadan kadan. Amma da sauki,mamma ya sunan dad din nawa? Ke daya ce a wajensa ne? Waye wannan nuran shima d'anki ne?" Mamma tayi dariya "Tambaya uku lokaci d'aya?" Baby tayi dariya itama "Allah kuwa mamma ke d'ince duk kin chanja kin k'ara kyau kamar baki da kishiya." Ta fada don a zatonta wannan katon gidan bazai yiwu ace mata daya ciki ba. Kuma daman a baya gwaggo Hajara ta fadamata yana da iyali. "Kema kinyi chanjawar data bani mamaki tasleem,kamar ba 'yar makaranta ba anya kina karatun ma?" Mamma ta fada tana binta da kallon zargi. Tasleem ta diririce sai kuma ta basar da sakin 'yar dariya,mamma tayi tagumi ganin d'iyartata harda b'ulin hanci haka kawai jikinta yayi sanyi duk da tasan kwalliya ce. "Kai mamma,muda muke karatu. Kuma fa shekara nawa rabonmu da juna kinga dole fa na chanja maki. Don Allah gayamin mamma." Mamma ta sauke ajiyar zuciya "Alhaji Kamal Hassan sunansa,kafin ya aureni yana da mace guda daya,Hajiya Aisha. Tana da yaranta manyan maza biyu,suna karatu a turai,sai budurwa d'aya,tana aure a Minna. Sai kuma nura wanda a wajen haihuwarsa Allah Ya dauki ranta. Tun bayan rasuwarta Alhaji yak'i aure har Allah Ya kawo mutuwar aurena ya amince zai aureni bayan da yazo gaida Liman ya ganni yace yana so. Humaira sunan matarsa taci muke kiranta hakan. Kinji tambayarki. Inaso kema ki amsamin tawa tambayar. Menene ainahin abunda ke faruwa? Jikina yana bani akwai abunda keda Abdullah kuke b'oyemin,hakanan nayi mamaki don ko d'azu munyi waya dashi bai bani labarin zuwanki Kazaure ba. Ya cemin mahaifinki na kwance tsawon watanni biyu baijin dadi shine ke d'awainiya dashi,duk sadda na tambayeshi ko kinzo dubashi daga makaranta sai ya hau yimin kame kame. Tasleem ko bakwa jituwa da yayan naki ne?" Zufa ta karyowa Tasleem,gabanta ya hau dukan uku uku. Shigowar Nura da sallama itace ta ceceta "Anti kizo inji dad." Mamma tayi azamar mikewa "Ina zuwa." Tayi gaba wanda hakan yasa tasleem sauke ajiyar zuciya. Amma rashin gaskiya ma baiyi ba. Hawayenta suka kwaranyo,wannan wane irin bala'i ne haka? Ita kam ko za'a kasheta bazata fadi komai ba ko don gargadin yayan nata ala barshi shi da bakinsa ya fad'a d'in. Waya ce ta soma k'ara,ta duba taga mai kiran. "Abdullah1" Bata d'aga ma ta ajiye. Har yayi ya katse. Haka ya jera kira har uku shiru sannan ya hakura. Tana nan zaune tana tunane tunane har Mamma ta k'ara shigowa tare da Humaira. Ganin wayarta na blinking ya fahimtar da ita anyi kiranta ne. Ta dauka ta duba,murmushi tayi mai ma'anoni tana duban Tasleem wacce ganinta yasa ta d'agowa daga kwanciyar da tayi idanunta bai bar fidda ruwan hawayen ba. "Ko yanzu kadai maganata ta fito." Ta zauna tana mai daure fuskarta tamau ta zauna kan gadon "Humaira tafi wajen gwaggo kuyi hira." Ba musu yarinyar ta fice a guje,tasleem kallo daya ta yiwa mahaifiyarta tasan babu wasa a tattare da ita "Baki da wacce ta fini duk duniyar nan,baki da wacce zaki kaiwa kukanta a duniya ta baki shawara wacce ni bazan iya baki ba. Tun rabuwata daku bana bacci mai dadi tasleem. Ga yawan mafarkai da nakeyi da lamuranki,haka kawai hankalina bai kwanta ba akan irin rufeni da Abdullah ke yawan yi idan na tambayeki. Ki fito ki gayamin hakikanin halin da rayuwarki ke ciki,naso na dauko ki alokacin da RALIYA ta rasu saidai kuma hakan bai samu ba sakamakon Abdullah daya cemin karatu kikeyi nima kuma alokacin Allah baiyi zanje gaisuwar ba. Wai menene ainahin abunda ke tafiya dangane dake?" "Raliya ta rasu?!! Ta maimaita a fili cike da tsananin mamaki. Tuni hawaye sun wanke fuskar Mamma "Baki kyautamin ba keda yayanki Tasleem,tambayarki ta kara fad'armin da gabana. Mutuwar Raliya baki da masaniya akai,rashin lafiyar abbanki baki sani ba,haihuwar yayanki da takwarar daya samar maki nan ba baki da labarinsa. Wannan wane irin al'amari ne mai d'aure kai? Tasleem ko guduwa kikayi daga gidan mahaifinki kika kasa hakuri har komai ya wuce??" Kawai sai baby ta fashe da kuka,toh ya ta iya? Mahaifiyarta ce fa. "Bazakiji komai daga bakina ba wallahi sai kinyi kiran yaya abdullah garin nan. Sai mun hadu mu uku sannan zanyi maganar dake bakina." Mamma tayi shiru tana kallonta har na tsawon mintuna kafin tayi azamar daukar wayarta tayi kiran Abdullah. Ya dauka ya soma gaisheta gami da tambayar ko lafiya ya kira ba'a d'aga ba? "Bana dakin,kanwarka ce a ciki." Bai taba kawo tasleem take nufi ba,a zatonsa ma Humaira ce. Mamma ta katseshi "Duk abunda kakeyi inaso ka ajiyeshi abdullah,gobe kazo kazaure inason ganinka." Yayi tsai kamar mai tunani sai kuma a sanyaye yace "Lafiya dai mamma?" "Lafiya lau,kazo dai nace." "Shikenan,in sha Allah ina nan tafe goben." Sukayi sallama. Mamma ta mike bata kara cewa komai ba ta fita. Ranar basuyi wata hirar arziki da diyarta ba kamar a farko ba itace ke d'okin ganinta ba...... ***** Gaba daya sun hadu a babban falon Daddy ciki kuwa harda Kb.....! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (51) Abba ne ya soma magana cikin nutsuwa "Kabir." Cikin sussunne kai ya amsa "Na'am Abba." "Jiya yarinyar nan muka ganta kwatsam ta dawo a motar kasuwa,koda muka tambayeta tace kaine kace ta dawo ba tare da ita kanta tasan dalilinka ba,gashi mun taru munason jin hakikanin matsalar data had'aku. Me tayi maka da zafi har haka?" Kabir ya saci kallon Yasmeen wacce akaci sa'a ita d'inma kallonsa takeyi. Kauda kai tayi gefe,jikinsa ya k'ara sanyi, ga kunya data dabaibayeshi. Toh me zaice? Lallai Yasmeen ta barshi a tsaka. "Wai bakaji ne ana magana sakaran banza da wofi!" Cewar Daddy cikin fusata. Yasmeen cikin kuka ta tare "Wallahi Daddy laifina ne,fad'a yayimin ni kuma nayi fushi nayi tahowa wata. Don Allah kayi hakuri Yaya kabir,ka gafarceni bazan k'ara ba don Allah." Haris ya runtse ido kansa a k'asa idanunsa sunyi jazur kirjinsa har d'agawa yakeyi saboda bacin rai. Ya saci kallon Kabir,duk alamun rashin gaskiya ya bayyana a fuskarsa. "Daman nasan kece marar gaskiya Yasmeen. Ni nasan d'ana bazai wulakantaki ba.." Cewar Abba. "Kada kayi saurin shaidar mutum mana Aliyu,idan anbi ta b'arawo abi ta mabi sahu. Alamun wannan shashashan sun nuna bashi da gaskiya. Idan ba haka ba kayi magana mana." Kabir ya daure kansa a k'asa yace "Gaskiyane Daddy,laifi tayimin nayi mata fad'a saidai banyi tsammanin zai mata ciwo har haka ba ta taho Kano bada sanina ba. Na yafemaki kema kuma ina fatan komai daya faru ya wuce,kuskure ne." Haris ya wurga mishi kallon raini,saidai baice komai ba. Abba yace komai ya wuce,nan ya k'ara yi musu fad'a akan hakuri da juna daga karshe yace su bari zuwa gobe su juya Abuja. "Na dawo kanka kai kuma,ya zancenka ya kwana?" Cewar Daddy. Haris ya k'ara russunar da kansa "Kamar yanda na fad'awa Daddy ne,Malam yace muje daku karshem sati yanason ganinmu ne." Daddy da Abba suka dubi juna,kafin Abba ya jinjina kai "Shikenan,Allah Ya kaimu asabar d'in." Aka amsa da amin kafin su sallamesu. Da sassarfa ya nufi wajen motarsa "Haris!!" Muryar KB ta dakatar dashi. Kamar bazai tsaya ba sai kuma ya tsaya ba tare da ya juyo ba. Ya karaso ya jingina da motar yana fuskantar Haris. "Nasan koda yasmeen ta boyewa kowa abunda ya had'amu,toh bazata boyemaka ba. Nayi laifi,please ka tayani bata hakuri." Haris yayi mai wani irin duba yana d'aga girarsa kadan "Ka kwantar da hankalinka dan uwana,yanda kaima ka shaidi Yasmeen da nuna maka soyayya tsantsa wacce ba algus hakika bazaka samu wata mishkila ba daga gareta..." Jin taku a d'an nesa dasu ya sanya Haris juyawa kafin ya dubi Kabir yana murmushi wanda tuni KB ya fahimci can k'asan nurmushin nan bacin rai da haushinsa ne tsantsa. "As i said,bazatayi fushi dakai ba koda kuwa zata kamaku turmi da tab'arya,ita d'in mai rufa asirinka ce. Sai kayi hattara KB,ba'a cutar irin wadannan matan a zauna lafiya." Daga haka ya kama handle na motarsa zai bud'e,KB fuska daure ya matsa,daidai lokacin Yasmeen ta k'araso. "Yayana tafiyarce?" Haris wanda ke kokarin sanya key ya dubeta yana murmushi cike yake da tausayinta "Tafiyarce kanwata,kada ki damu zan b'ullo kafin ku wuce. Hope bada wuri zaku tafi ba?" Ya maida akalar tambayar zuwa ga KB,KB ya d'an tab'e baki "Banajin da wuri zamu tafi, watakil ma sai zuwa jibi.." "Meyasa? Kaga fa ban taho da wasu kaya ba sosai,kuma Abba yace lallai gobe mu wuce." Ya watsa mata kallo kamar yayi magana sai kuma ya fasa, shi fa so yake ya nemi inda baby take. Ganin kallon da yayi mata yasa ta tsoraci fad'ansa tayi azamar cewa "Yayana saida safen." Tayi gaba da sauri saurinta,Haris ya dubeta kafin ya watsawa Kb kallo a wulakance,tuni idanunsa sun sauya "Baby ce ke neman shiga rayuwar aurenka kb,right?" Kb ya dubeshi a sanyaye,ya numfasa "Hakane Haris, saidai wallahi bansan meyasa na tsinci kaina da mugun kaunar yarinyar nan ba ni kaina bazance maka ga...." Figar motar da Haris yayi ne ya sanya Kb ja baya da sauri hakanan hon ya shigayi da karfinsa har Maigadi ya kammala bud'ewa ya fita. Yayi daidai da zuwan Abba da daddy. Abba ne zai shiga gidansa. Ganin yanda Haris ya fita,Abba yace "Kai Kabiru,menene ya faru?" Kb wanda tunani da mamakin yanda akan yasmeen amintarsa da dan uwansa ke neman samun mishkila duk ta hanashi motsi,jin maganar Abba ne yasa ya juyo. "Bansani ba Abba." "Allah Ya tsare hanya toh. Matarka nace ta shirya kuje can gidanka idan yaso zuwa gobe saiku wuce Abujan." Baiji dadin wannan hukuncin ba,saidai yasmeen ta biyashi data boye sirrinsa,tabbas idan yayi mata wani rashin adalcin bai kyauta ba. Ya amsa da toh kawai. Jimawa kadan ta fito suka wuce a mota sai janta yakeyi da hira ta basar dashi bisa hud'ubar mami da ta nuna mata ya dace ta d'an ja ajinta. **** Da sallama ya shigo gidan,humaira aguje ta rukunkumeshi tana ihu "Ga yaya! Ga Yaya!!" Wannan yayi sanadin tashin tasleem dake bacci a falon sakamakon damuwa ta haneta bacci daren jiya da kuma shariyar da Mamma tayi mata tabar wani d'okin ganinta gaba daya ma ta chanja mata fuska. Cak ya tsaya ita kuwa ta daure fuskarta tamau tayi azamar mikewa zata nufi falon sama,a guje yasha gabanta. Bakinsa na rawa,ya kasa gaskata cewar ita d'ince tsaye a gaban idonsa. Dakyar ya iya tab'a hannunta jin cewar ita d'ince yasa ya riko hannun hawaye sun wanke fuskarsa. Kawai sai ta soma kukan itama kafin ta warce hannunta tayi sama a guje har zuwa d'akin mamma da batanan tana dakin mijinta. Gadonta ta fad'a tana kukan tunowa da yanda yayan nata yayi mata korar kare daga gidansa. Muryarsa taji cikin kuka a kusa da ita "Na rasa kalar godiyar da zan yiwa Ubangiji,da ace kin kara shekara baki dawo ba wallahi mutuwa zanyi ko nima a nemeni a rasa. Tasleem kin jefa yayanki cikin tashin hankali,nayi magana cikin fushi na zartar da hukunci ban tab'a zaton zakiyimin haka ba. Tasleem ina kika shiga? Ya za'ayi ni Abdullah na yankewa kanwata abar kaunata wannan hukunci mai tsauri. Ina sunan 'yan uwantakanmu? Wallahi kusan zaucewa nayi dana wayi gari naga da gaske kin gujeni...." Mamma ya gani tsaye ta harde hannuwanta a saman kirjinta,hakanan ta zuba musu ido. Jin da tasleem tayi Abdullah yayi shiru yasa ta dago kai,taji k'arar rufe k'ofa wannan yasa itama ta dubi k'ofar. Mukulli mamma ta saka daman mijinta ya fita zuwa aiki,humaira tayi umarni ga gwaggo mai aikinta ta mik'ata gidan liman. Nura kuwa makaranta yake zuwa baya dawowa sai yamma sakamakon shirin jarabawar karshe na sakandire da yakeyi. Gidan ya zamana daga Mamma sai yaranta mafi soyuwa azuciyarta. Fuska a daure ta zauna yayin data dubesu "Ku zauna sosai." Tasleem ta mike zaune daga kwanciyar da tayi,shima abdullah ya zauna gefenta a saman gadon,yayinda mamma taja kujerar gaban madubinta ta zauna idanunta a kansu. Ta dubi tasleem "Kince sai yayanki yazo zaki fadamin abunda ya afku a rayuwarki ko? Yau kuma gani gaki,gashi muna sauraronki duka." ''YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (52) Yau ba ranar boye boye bace, ita kam koda zata boyewa kowa matsalarta toh banda mahaifiyarta. Don haka ta russunar da kanta ta labartawa mamma halin data tsinci kanta tun rabuwarsu. Da kuma fyaden da Usman yayi mata wanda ya sanya mamma fashewa da kuka,Yaya Abdullah kuwa tsananin mamakin yanda akayi kanwarsa bata sanar dashi bane ya cikashi. "Haba Tasleem,meyasa kiks boyemin magana har haka?" Tayi murmushi duk da ruwan hawayen da take fitarwa "Yaya baka nemi hakan daga gareni ba. A karshe ma saika kama maganar su Raliya ka yarda cewa na bawa wani budurcina. Haba yaya, wane talauci ne zaisa nayi haka?" Ta ja majina kafin ta dora,haka har ta gangaro kan rayuwarta a hannun yayanta da kuma rud'in shaidan da yasa ta bawa rilwan jikinta da cikin data samu yayanta ya koreta. Haduwarta da Momi harma da barikancin data fad'a har zuwa taimakon da haris yayi mata bayan tayi hatsari da zuwansu nan. Hakanan bata b'oyemusu ko wanene haris ba saidai bata tonawa kb asiri ba. Salatin da Mamma ta doka ne ya maido hankalinsu gareta,tuni kuma ta kife a k'asa sumammiya. Ihu tasleem ta fasa,Yaya abdullah kuwa yayi yunkurin fadawa bandaki ya debo ruwa. Baiyi wani jinkiri ba ya yayyafawa mamma amma ina bata motsa ba. Tasleem tana ihun kiran sunanta tana fadin "Mamma kimin aikin gafara,wallahi mamma ni ba 'YAR BARIKI bace yanzu. Mamma mutuwarki mutuwata ce..." "B'udemin kofar nan da sauri." Yaya abdullah ya fada lokacin da yake kokarin daukar mamma. Da gudu tasleem ta bude kofar,tuni yayo waje yana fadin "Ki biyoni da hijabin mamma." Ta wulk'a idonta,ta kasa gane hijabin ma kawai saita janyo farin abu dake rataye jikin hanger. Yaya abdullah ya ajiye mamma a baya jikinsa a sake yana kuka. Ganin haka tasleem tayi azamar zagayawa ta shiga mazaunin direba ta tada motar. Da gudu maigadin dake kallonsu ya bude kofar ta fita shaf batajin radadin hannunta tama manta tana da ciwo saboda tsabar Firgicin da take ciki. "Yaya ina ne asibitin,ka gayamin kada ka janyo mu rasa mamma." Yayi ta maza ya dunga gwada mata hanya har suka iso. Da gaggawa aka amshesu akayi ciki da mamma. Tasleem kawai ta zube a bakin kofar ta hada kai da gwuiwa tana kuka sosai. Yayanta ya iso ya zauna kujerar dake gefanta,hakan ya bata damar kwantar da kai a cinyarsa "Yayana na halaka!" Ya dafa kanta ya shiga girgiza kai saidai ya kasa magana. Ta dago ta dubeshi "Idan mamma ta mutu wallahi nima mutuwa zanyi. Rayuwata bata da amfani,dana sani da nadama sun dabaibayeni fin tsammaninka yayana,meya rud'eni da bariki? Menene shi? Mena d'and'ana cikinsa? Wallahi yaya abdullah rayuwata bata da amfani,wani wanda baida uwa da uban ya fini. Amma yayana kaima kasan bani da laifi ko? Khalid Ma'aruf waziri shine ya watsar dani. Bayasona,bai damu da sauke hakkin daya rataya a wuyansa a kaina ba. Wallahi bana sonshi,na tsaneshi nima. Bayamin fad'a,bayamin nasiha,ya kasa aurar dani. Na tsaneshi!!!" Sai ta mike tana ihu kafin ta hau buga kanta da bango,yaya abdullah ya damk'eta a gigice,mutanen wajen ma sai salati sukeyi suna kiran lafiya kuwa? Kawai saita suma jikin yayan nata......! ''YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (53) "Tasleem!!" Yaya abdullah ya fadi da k'arfi sannan ya dubi mutanen wajen gumi duk ya gama wankeshi hadi da hawaye kwance saman fuskarsa. "Ku taimakamin don Allah." Sai ga wata nos, tayi azamar kama tasleem ita da wata mace dake a layin ganin likita suka shiga ta kwantar da ita saman gado sannan ta kirayi likita. Nan suka soma kokarin ganin ta farfad'o. Yana nan tsaye likitan dake tsaye kan mamma ya fito "Alhamdulillah,ta farfado har ma tana nemanku. Kuna iya shiga,ina ita kanwartaka?" Yaya abdullah ya numfasa yana hamdala kafin ya nunamishi d'akin da aka sanyata "Ta suma ne amma likita yana tsaye a kanta." Cikin damuwa likitan ya nufi dakin da baby take bayan ya damkawa abdullah takardar magungunan da za'a siyo ya kuma tabbatar mishi hawan jininta ne ya tashi amma da sauki,shi kuwa abdullah yayi azamar fad'awa d'akin da mamma take. Tana kwance ta kurawa silin ido,jin shigowar mutum yasa ta duban kofa kafin ta yunkura ta mike zaune,gaba daya tayi mugun sanyi ga hawaye na zubo mata. Abdullah ya zauna yana mai rike hannunta "Sannu mamma." Ta gyadamishi kanta kawai,kafin ta hau duban hanya, cikin rawar murya ta tambayeshi "Ina tasleem?" Ganin halin da take ciki yayi nufin rufeta,ta girgiza mishi kai "Banda yau Abdullah,kabar k'ara b'oyemin komai ga rayuwarku. Idan ka boyemin taka,kada ka kara cutata da karemin damuwar diyata mace." Hankalin abdullah ya tashi "Ki gafarceni mamma,wallahi ban tab'a rufeki domin cutar rayuwar kanwata ba. Asalima bacin raine yasa na kori tasleem daga gidana wanda daga baya nayi muguwar dana sani bayan kuma da komai ya fito. Mahaifin rilwan ya sameni ya sanar dani batun wasikar,harma ya nemi a daura aurensu anan ne hankalinmu ya tashi." Ya zame ya durkusa gwuiwoyinsa a k'asa yana hawaye jikinsa kuwa har kakkarwa yakeyi "Ki gafarceni Mamma,bansan zan cuci rayuwar kanwata ba da ban aikata wannan mummunan laifin ba. Saidai ganinta da ciki ya rud'amin kwakwalwa har ma na kasa wani kwakkwaran tunani. Na tsoraci kada ta rusa aurenki ne,ganin da nazo nayi maki kina cikin kwanciyar hankali da walwalar dana jima ban riskeki cikinta ba mamma. Bayan haka kuma ina...." "Kiyi a hankali mana." Jin muryar nos duk suka mayarda hankulansu ga kofar shigowar. Tasleem ce gaba dayanta a hargitse gashin kanta na usuli wanda bana k'ari ba duk ya barbazu a kafad'arta ko dankwalin babu. Ga bandaji da aka zagaye goshinta dashi sakamakon jinin dake fita daga goshin nata.Ta ja burki wanda ya janyo nos dinma tsayawa kafin kuma ta fita ta rufe musu kofa ganin kamar ba'a bukatarta a wajen. Kunya da nadama tsantsa suka kasa barin Tasleem k'arasawa ga mahaifiyarta. Meyasa alokacin data tashi yin wannan aika aikar na zina duk basu fad'omata ba? Babban tashin hankalin ma,mantawa da tayi da Mahaliccinta kuma alhamdulillah kullum cikin tuba take hakanan yanzu hakan ma haila takeyi. Zubewa tayi anan tana mai sanya tafukan hannunta ta rufe fuskarta tana kuka kamar ranta zai fita. "Astagfirullah! Astagfirullah." Tayi ta maimaitawa har babu adadi,mamma kallo daya tayi gareta bata k'ara ba. Koda taji tausayin diyarta da kaddararran rayuwar da tayi a baya batajin zata iya saukowa a daidai wannan lokacin da bacin rai da tsoron tambayar da Allah zaiyi gareta akan amanar daya damk'a mata na d'iya babu abunda ke yawo a kwanyarta. Ta saki hannun abdullah bayan data dubeshi "Maidani gidan mijina." Wannan ya tsayar da tasle daga kukanta,a gaban idonta mamma ta kunce dankwalinta ta d'an rufawa jikinta tayi waje. Abdullah ya dauki takardar maganin ganin mamma na shirin fita tayi saurin rike kafarta "Don Allah mamma ki yafemin. Nayi kuskure bazan kara maimaita irinsa ba." Bata ko saurareta na ta janye kafarta tayi hanyar fita,da sauri abdullah ya ciro takalman kafarsa ya ajiye kusa da kafafunta "Ki sanya Mamma,kada ki fita haka." Ta sanya tana mai k'ara jin kaunar yaran nata a zuciyarta. Saidai kuma sunyi laifi gareta. Tabbas ta k'ara hakikancewa Dr. Khalid bashi da amana. Suka fita, abdullah saida ya bari mamma tayi gaba ya bude mata motar ta shiga kafin yazo ya rarrashi baby itama ta mike tayi gaba sannan yaje ya share bill nasu,likitan yana kara jaddada mishi cewar a kula da abunda zai k'ara tab'a zuciyar mamma saboda blood pressure dinta kada yayi high. A mota shiru,ba wanda ya cewa wani uffan tsakanin mamma da baby domin mamma zaune take a gidan gaba. Abdullah ya dawo "Ki gafarceni mamma,na tsaya karb'o magani ne." Batace uffan ba yaja sukayi gaba. Suna zuwa gidan sukayi kicibus da Dad yayi ribas zai fito,ganinsu yasa shi komawa. Suka fito ya nufosu a gigice yana kama kafadun mamma. "Maman nura lafiya dai? Maigadi ke sanarmin kuna asibiti dawowata kenan." Ya dubi abdullah sannan Tasleem yayi mamakin halin da suke ciki. "Ita kuwa d'iyata menene ya sami goshinta?" Da sauri Mamma ta tare "Lafiya,hawan jinina ne ya d'an motsa shiyasa suka kaini asibiti ba'a hayyacina ba. Bakaga yanda yaran naka suka rud'e ba?" Baby ta amshe "Dad buguwa nayi wajen sauko da mamma daga steps." Ya danyi murmushi ya amince da hakan "Wayyo sannunki diyata." Ya maida dubansa ga matarsa wacce kallonta ke mantar dashi komai "Nagode Allah da ya ceci ran abar kaunata." Daga haka yaja hannunta zuwa ciki yana sannu sannu ba iyaka. Baby ta daskare tana dubansa cike da sha'awa. "Tell me now my sister,ta yaya zan bari matsala ta b'ullo tsakanin dad da mamma?' Ta dubi yayan nata wanda ke magana cike da matsanancin damuwa hannunsa rike da ledar magunguna. Hawayenta suka cigaba da kwaranya tayi murmushi mai ciwo "Babu." Ya numfasa kafin yaja hannunta "Inason mu zauna mu tattauna dake sosai." Daga haka yaja hannunta suka mara musu baya. Sam mamma tak'i bawa tasleem damar yin magana da ita a keb'ance. Tun magrib tayi sashen mijinta domin yace ta huta bayason ganinta a kicin. Shima can ya tare a wajenta. Abdullah yace mishi sai zuwa gobe zai koma. Tana zaune ta idar da salla ta zubawa talabijin ido inda humaira ke kallon tashar Disney na cartoons zallah. Ta lula cikin tunanin wannan shariyar da mamma keyi mata,Abdullah ya zauna kusa da ita saman kujera yayinda take zaune kan darduma ta takure. "Biyoni." Ta bishi babu musu har zuwa d'ayan falon dake jikin wanda suke. Bayan sun zauna ya dubeta......! YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (54) Saidai ya soma da bata hakuri laifin daya aikata gareta na korarta daga gida da kuma gargadinta da zuwa wajen mahaifiyarsu kafin yayi mata nasiha ya kuma nuna mata kurenta na rashin dacewar jefa kanta a karuwanci da tayi. Koda suka gangaro kan Mamma,ya shawarceta data koma gidan liman ta bari har zuwa sadda mamma zata sauko hakanan jininta ya daidaitu. Tasleem tayi na'am da wannan,saida ya kammala da wannan babin kafin ya kirayi sunanta wanda hakan ya sanyata dago kai ta dubeshi tana mai amsawa. "Ya dace ki sassauta kiyayya ga mahaifinki." Nan da nan ta daure fuska tamau,ya share kamar bai gani ba ya cigaba da magana. "Mahaifinki a yanzu idan kika ganshi,kikaga yanda yake fama da ciwon sugar da hawan jini,zaki tausaya mishi saboda ramar da yayi tayi yawa,aikinsa tuni ya ajiyeshi gefe. Zakiyi mamaki idan nace maki kullum cikin zubar hawaye yake duk a dalilin rashin sanin takamaiman inda kike. Ban boyemishi dukkan abunda ya faru ba ya nunamin kurena,yace idan shi ya koreki ba'a hayyacinsa na meyasa zanyi wannan ta'asar? A karshe yace laifin nashi ne. Da ace bai koreki ba babu yanda za'ayi ki shiga wata rayuwa ta daban." "Yaya bani labari mana game da abunda ya kawo chanjin Abba." "Tun bayan tafiyarki da watanni uku, mummunan iftila'i ya fad'awa Usman na konewar babban shagon da baiyi ko wata biyar da bud'ewa ba,hakanan wasu b'arayin sun tareshi a hanya sun mishi duka har suka nakastashi suka kwace wayoyi da kudadensa. Abun mamaki kuma sati ba'a rufa na itama marigayi raliya akayi hada mata jini da majina a karshe aka watsar da ita a kofar gida. Jinyar da tayi kamar bazata tashi ba,gashi kuma wata kaddarar komai na Abba ya soma ja da baya Tasleem. Kamar wanda aka sanyawa hannu fitar ma da yake zuwa asibitinsa ya gaza. Hakanan raliya ta matsa mishi akan sai an fidda d'anta waje anyi mishi aiki saboda tuni matarsa tace bazata iya zama da nakasashshe ba ta ajiye mishi 'yar sa ta tafi. Akan dole Abba ya kashe makudan kudade wajen aikin kafar Usman ta hanyar fitar dashi waje saidai aiki baiyi ba wai a niyyarsu a sanyamishi kafafun roba saidai garin haka mutuwa ta riskeshi acan. Nan raliya ta hau ihu da zage zage,abun ne ya zame mata wajen goma ba. A gefe ga d'iyarta ta tsunduma kanta a harkar bin maza itama. Can kuwa nura ne ya kara lalacewa da bin mata. Matarsa ma ta gujeshi,hamza kuwa ya zamo mijin tace a wajen matarsa. Ke rayuwa fa tayi mata zafi ga mutuwar Usman,haka ta dawo ta rungumi jikokinta da suke a wajenta. Bata isa ta sanya Hamida da Hamid aiki ba suyi,kamar wata sa'arsu haka zakiga sunayi mata tsawa. Duk cikinsu,hindatu kadai ta fita daban,babu ruwanta ke sai kice ma ba daga jikin raliya ta fito ba. Nazo jana'izar Usman sannan na tattara na koma Abuja ina mai cike da dumbin mamakin ramar da Abba yayi sannan gaba daya duk yayi sanyi kamar bashi ba. Wata biyu rabona dashi saidai nakan kokarta kiranshi na gaisheshi,wataranar juma'a ina zaune na dawo daga masallaci na amsa kiransa inda ya nemi nazo na sameshi da sauri. Ba shiri washegari na tafi a mota. Kuka sosai na samu Abba yana yi,cike da fargaba nikam na karasa wajenshi don gani nakeyi kamar zai yimin magana cikin fada fada kamar yanda ya saba. Ga mamakina naga ya rungumeni yana neman gafarata,yace a baya yakan damu idan yayimana wani abun ashe ba'a son ransa yakeyi ba Tasleem. Yace min ya iske raliya tana waya da bokanta inda takeso tazo ayi mata aikin da za'a kasheshi suci ragowar kudinsa saboda ta fahimci ya soma talaucewa ita kam bata tab'a ganin jinin sarauta mai bak'in jini kamar Khalid ba. Kowa gudunsa yakeyi yan uwan duk sun juyamishi baya saboda ganin shi kadai ne ba uwa ba uba.(Ta manta itace ta janyomishi tsanar,don akwai randa yayansa waziri yana son ganinsa yace bai zuwa. Kusan sati shiru har da kanshi wazirin yazo gidan,ganin babban mutum yasa maigadin budemishi dakin bak'i,yayita zaman jira amma raliya ta rike abba ta hanashi fitowa a karshe waziri ya fusata yabar gidan da alkawarin bazai kara shiga harkar Khalid na tunda bashi da bukatarsu hakanan ya gargadi dukkam zuri'arsu kada wanda ya k'ara lek'awa gidansa. Wannan labarin nima baba Maigadi ke bani,hankalina ya tashi don har gidan waziri naje na bashi hakuri ya sakarmin fuska sosai ya nunamin ai mu d'in nasu ne. Yace kuma zai sanya ayi addu'a sosai gareshi don bai amince da yanayinsa ba. Shima ya d'agawa mahaifinmu kafa ne har zuwa wani lokacin. Abba ya cigaba da labartamin,yace tun sadda yaji wannan zancen yaji kamar bashi ba,komai na rayuwarsa ya daidaita,kirjinsa yabar nauyi. A ranar kuwa ya yiwa raliya abunda bai tab'a yinsa ba sakamakon tsanarta da yaji,duka yayi mata sosai sannan ya saketa. Tace wallahi bazata bar gidan ba,saida ya hado da jami'an tsaro har jikokinta yace duk ta tattara ta tafi dasu shi kam baisan menene ya kwasheshi ya auro wannan kaddarar ba. Hakanan ya kori nura wanda har ya nemi ya zageshi. Hindatu kam tasha kuka,ta hau rokonsa ya barta a wajensa itama ta tsani uwarta. Haka dai ya hakura yabar yaransa. Washegarin faruwar al'amarin ne yayi kirana yake sanar dani. Nayi godiya ga Allah da baisa zan mutu kafin wannan rana ba. Nan Abba ya tambayeni game da mamma,na bashi labarin komai har zuwa gidana da kikayi da sauransu. Anan ne nadama tsantsa ya kamashi. Tun dai daga lokacin ya kamu da rashin lafiya,karshe yasa na kaishi wajen waziri. Muna shiga waziri yana zaune a fada,yana ganin Abba cikin yanayin zubar hawaye yana nufoshi,tsam ya mike har na tsoraci ko marinsa zaiyi kawai sai ya rungumeshi wanda hakan ya bawa abba kuka sosai a jikinsa. Ya jashi inda fadawan suka mike suna zuba kirari,sukayi ciki. Kinji yanda aka sasanta,Abba ya tsanantawa su Hamid ya hanasu fita ko'ina ya santa ido sosai a kansu,ganin batanci da rashin maida hankalin Hamid a karatu zaiyi yawa yasa shi turashi makarantar horo. Hamida kuwa kasancewar tana tsoron abba alokacin ganin irin korar da yayiwa mamanta sannan taje taga muhallin da raliya take babu wani kayan morewa rayuwa dolenta ta nutsu,Abba yace ya bata sari ta fiddo miji ko kuma ya aurar da ita ga wanda yaso. Har nan kazaure na rakoshi ya roki gafararsu kafin ya koma kuma rashin lafiya ta hau shi. Yayimin fadan dalilina na boyewa iyayen mamma inda kike karshe abba ya hau yawaita addua da tsayuwar dare da kuma zubar hawaye duk saboda rashinki da alhakin daya dauka namu. Raliya kuwa gobara sukayi a gidan babu wanda ya tsira daidai da nura,sakamakon jonin wuta direct da Nura yayo musu acewarsa bazai iya rayuwa ba wutar lantarki ba ya gama zage mahaifiyarsu tas akan bakin cikin data janyomusu suna cikin daula. Karshensu kenan. Yanzu haka hamida tayi aure ga wani alhaji mai mata biyu har ta haihu,duk da wulakancin da take sha hakanan take zaman hakuri. Hindatu kuwa tana nan tare dani a Abuja ta soma karatunta a jami'a, hakanan Abba da nake jinyarsa saidai yanzun jikinsa da sauki sosai. Waziri ma ya matsamin na maidoshi gabansa inajin hakan zaiyi tunda shima Abban yace ya gaji da zama gidana saboda kunyar hasina. Duk da dai yanzu gidane na kashin kaina." Tasleem tayi shiru,tabbas rayuwa abar tsoro ce. A sanyaye ta kara tambayarsa "Ina labarin Ridwan kuma?" Murmushi Abdullah yayi "Allah Sarki,abbansa fa ya jima yana fushi dashi har korarsa yaso yi na hana. Amma yanzu yayi aure yana zaune acan London wajen uncle dinsa da matarsa Jidda. Yaransu biyu ma,daya taci sunanki dayar kuwa sunan mamansa." Tayi murmushi kawai. ***** Washegari yaya abdullah yana tafiya,itama ta shirya koda ta yiwa mamma sallamar komawa wajensu inna bata ko kalleta ba. Haka nan ta wuce a sanyaye. Da la'asar Liman ya tura ayi kiranta.....! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar (55) Bata kawo komai ba ta mike ta yafa mayafinta ta nufi dakin Liman jikinta akwai yanayin sanyi wanda tun dawowarta daga gidan mamma take cikinsa. Koda inna ta tambayeta ta amsa da babu komai. Yana zaune yana duba wani littafi na hadisai yaji sallamarta wanda hakan yasa shi ajiye littafin a gefe yana mai amsawa fuska a sake. Ta shigo tana yamutsa fuska kadan kafin ta soma kokarin zama tana fad'in "Nidai wannan tsohon kana neman matsamin fa,yanzu kuma menayi aka d'agoni bama a tarbeni da 'yar shila ba." Yayi dariya "Shak'iyiya,wanda kika ci bai isheki bane a k'aro maki gobe? Nutsu don magana zamuyi." Ya soma da yi mata doguwar nasiha akan muhimmancin aure wanda tun daga haka tasha jinin jikinta,kirjinta kuma bai bar bugu da sauri da sauri ba. Saida ya kammala sannan ya bijiro mata da bukatarsa na neman amincewarta kan batun aurenta da Haris. Cikin tsananin mamaki da fargaba ta dubeshi "Shi Haris dinne yace yana sona baffa?" Jin dadi game da amsar da zai bata yasa Liman yin wata 'yar dariya "Shakka babu,harisu ne yazo da batun kamar yasan fatanmu kenan ni da aminina. Kuma munyi na'am da batunsa nasan bazaki watsa mana k'asa a ido ba kasancewarki yarinya mai biyayya." Tayi k'asa da kanta,nan da nan abokan hirarta suka ziyarci fuskarta(hawaye). Ina ita ina Haris wai? Haris yasan abunda yake kuwa? Me zaiyi da sauran maza? Sam bazata bari ta cuci mai niyyar taimakonta ba,kai ta kasa gaskata da gasken shine yayi tayin auren nata. "Kuyi hakuri bafamfa,bazan iya aurensa ba!" Nan take annurin dake saman fuskarsa ya dauke,tamkar bai taba dariya ba ya koma Abdulmaleek Hussein dinsa sak! "Nufinki zaki bani kunya ne Tasleem? Toh bari na fadamaki wallahi tunda nake da Aminina tun zamanin kuruciyarmu dayanmu bai taba zuwar wa dayanmu da bukata ba munyi watsi da ita. Baki isa ba Tasleem! Ko uwarki k'arya takeyi na nemi bukata awajenta tak'iyi,na takaice maki ma aminina shine ya wuce gaba wajen aurenta da Ubanki tun a farko domin a baya banso tayi nesa har haka ba. Ki tashi ki barmin d'akina,aure kuwa keda Harisu saidai idan anyishi ki mutu." Daga haka ya maida fuskarsa gefe babu wata walwala a samanta. A sanyaye tasleem ta mike tana k'ara mannewa da abokin hirarta harda sheshshek'a. Kallo daya tayi mata kafin tabar murza robb a hancinta "Lafiya kuwa?" Cikin kukan dai ta labarta mata yanda sukayi da Liman,inna taja tsaki gami da fadin "Allah Ya kyauta,ina goyon bayan Liman,wannan hukuncin yayi. Domin kuwa samun yaron mutunci irin Harisu a zamanin nan akwai wuya. Nikam dari bisa dari na amince kuma banga aibu da aurenku ba. Budurwa sharab dake,ai wallahi sai yanda kikayi dashi ta hanyar biyayya da kissar d'iya mace." Ji tayi tamkar magana take yab'a mata,da sauri ta mike ra shuri takalmanta batayi wata wata ba ta fada gidan gwaggo Hajara bazata kwana a gidan ba. Meyasa Haris zaiyiwa rayuwarsa haka? Duk a zatonta jihadi yake niyyar yi don tausayinta batasan kudurin da Haris ke shirin yi ba. Gwaggo Hajara ma yabo da hamdala ta shiga yi,ai ita kam tun farkon ganinta da Haris takeso aure ya kullu tsakaninsu sai gashi Allah Ya amsa. Nan tayita lallashin tasleem gami dayi mata nuni akan illar bijirewa umarnin babba. ****** "Nayi zaton ai da Zahra za'a hadashi?" Murmushi Malam yayi kafin ya bata amsa "Ya kike wata magana kubra? Da Zahra da Tasleem basu da wani bambanci a wajena. Tunda yaro ya nuna yanason Tasleem sai a bisu da addu'a inajin hakan zaifi." Ba haka taso ba sanin da tayi Zahra ita kadai take iya gayawa sirrinta,kuma ta tabbatar mata cewar tana son Haris. Bata hakura na dai ta k'ara muskutawa "Malam fadamaka ne banyi ba amma hakikanin gaskiya Zahra banda alkunya ya hanata magana tana son Haris kwarai dagaske,mezai hana a had'a mishi su biyu duka a aura mishi na tabbata Harisu bazai watsa mana k'asa a ido ba." Malam ya dubi hajja kubra a mamakince "Harisun ya gayamaki yana da ra'ayin mata biyu da wurwuri haka ne?" Ta girgiza kai,zatayi magana ya dakatar da ita "Bazan hanaki abunda kikaga zaifi ba,saidai ni da kaina bazan tunkari Harisu da zancen ba. Ki tuntub'eshi da kanki idan yaga zai iya toh nawa bai wuce daura aure ba." Ranta ya d'anyi sanyi jin hakan. Tana matukar kaunar Zahra,bata tab'a tsayawa kula samari ba sai gashi rana tsaka ta kamu da son Haris wanda har ta kasa b'oye mata ita kuwa mezaisa ta kasa yin wannan kokarin gareta? "Shikenan Malam,Allah Ya zab'a abunda yafi alheri. Zan gwada hakan." "Ameen." Kawai yace mata kafin ya nemi ta kawomishi furarsa. ****** Momi tayi wani murmushi kafin ta rausaya idanuwa "Ka kwantar da hankalinka Kb,na tabbatar maka baby zata dawo. Bata komai saida shawarata. Koda ya tabbata auren zatayi na tabbatar maka da cewar zata nemeni bada jimawa ba. Nima ban sameta a waya ba,saidai nasan wacece baby tunda har ta furta maka tabar wannan harkar tabbas da gaske takeyi. Mu kuwa a sharuddan kungiyar,lallai idan mace zata bar harka sai ta tattaro mana dukkan kadarar data mallaka cikin harka idan kuwa ba haka ba zamu hanata auren gaba daya muyi sanadiyyar gurb'acewar dukkanin rayuwarta wanda nake da yak'inin Baby bazata iya ba. Yanzu kawai mu jirayi dawowarta." Kabir ya jefa hannu aljihu ya zaro bandiran kudi 'yan dari bibbiyu har uku ya dire a kusa da Momy yana murmushi "Ga wannan asha ruwa,burina ta dawo na ganta." Tana taunar cingam gami da wani irin murmushi na duniyanci ta dauki kudin a wulakance tana juyawa kafin ta watsa mishi kallo tana fari da ido "Bukatarka zata biya da zarar Baby ta dawo. Zanbi kowacce hanya don ganin ta amince da aurenka." Ya shafi suma yana dariya kafin ya jinjinawa Momy "Dakyau momynmu,anjima zanbi jirgi zuwa Abuja,sai naji wayarki." Daga haka yasa kai ya fice yayinda Momy ta bishi da murmushi na musamman. 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (56) Kwance yake akan restingchair a farfajiyar gidansa daga can poolside. Idanunsa a lumshe fuskarsa ma'abociyar kyau da kwarjini sai shek'i takeyi. Yammacin juma'a ne,garin yayi luf luf sai wani ni'imantaccen iska ke busowa da kamshin k'asa kasancewar da safiyar yau din anyi ruwa sosai. Sanye yake da jar t-shirt,da wando wanda da kad'an ya rufe gwuiwoyinsa. Sallamar isah mai gadinsa ne ya sanyashi bude idanunsa yana mai amsawa bayan yayi kokarin danne damuwar dake shimfide kasan ransa. "Yallabai kayi bak'o yace a sanar dakai cewa Deen Bukar ne." Jin sunan wanda ya jima baiji daga gareshi ba ya dago yana murmushi "Kayi mishi iznin shigowa isah." Matsakaicin saurayi ne,mai d'an kiba. Yana sanye da kananun kaya shima,kallo d'aya zakayiwa bak'ar fatarsa ka fahimci yana hutawa sakamakon lukui lukui da tayi. Ganinsa yasa Haris mikewa tsaye yana bayyana hakoransa a waje cike da farin cikin ganin oldclassmate dinsa na Malaysia. Deen Bukar. Rungume juna sukayi suna masu dariya kafin su cafke. "Shegen sama,deen kana hutawarka,irin wannan k'iba kamar ba soja ba?" Deen yayi dariya yana nunoshi da yatsa "Zaka fara ko Gent? Toh ai kaine za'ace baka aikin komai. Ka ganka kuwa?" Sukayi dariya kafin Haris ya dauki wayoyinsa da tab "Bismillah." Suna tafe suna hira har suka shiga falon Haris wanda ya k'ayatu iya k'ayatuwa. Haris yayi kiran kuku dinsa,Henry. Ya sanyashi ya kawowa bak'onshi abun motsa baki. Bayan tafiyar henry ya dubi deen "Sai fa hakuri kasan abunka da gwauro." Deen yayi dariya "Kai ka sowa kanka,ya dace ka nemo mana mata musha biki. Gashi dai twins dinka(yaran deen) suna k'ara girma. Kb fa,ya labarinsa?" Haris yayi dariyar yak'e "Yana nan da bebinsa d'aya,Nasreen." Deen ya jinjina kai lokacin Henry ya iso ya soma zuba mishi juice a kofi. "Banji dadin rashin aurenka Gent,ko still now tsoron matan kakeyi?" Haris yayi murmushi "Aure lokaci ne Deen, sannan idan nace ma ina tsoron matan na yanzu ai ba laifi bane." "Magana ta fito,kacemin kawai tsoronsu kakeyi." Murmushin dai Haris ya k'ara yi kawai,shi kadai yasan matsalarsa. Duk sadda ya tunano da tafiyarsu kazaure a gobe damuwa kadai ke dabaibaye zuciyarsa. "Last two months ai,inajin 5th of may ne,na hadu da wani kamar KB naka a Ni'ima hotel da wata baby. Naso nayi mishi magana duk da dai ina kokwanton ko shi d'inne tunda kaga bazan kawo har yanzu KB yana yayin wasu bebs din ba tunda he's married. Kafin ma nakai wajensu sunyi gaba,na rako oganmu ne wajen wani abokinsa. Saidai yanzu kace yana ina ma?" Haris ya kara zuciya da lamuran KB, yana kara jin kwarin gwuiwar auren Baby don ya fahimci ita kadai ce yake tarayya da ita yanzu. A zahiri ya murmusa "Hum, bana zaton shi ka gani dai,mutumin dake zaune a Abuja ba." Deen ya tabe baki yana mai daga kafada kadan "Zai iya yiwuwa." Daga nan suka share zancen,zuwan Deen shi ya mantar da Haris damuwarsa sukayita hira yana bashi labarin yanda wasu rundunarsu ke fama da matsalar boko haram,bai bar gidan ba saida sukaci girkin henry. Bayan magriba ya wuce. ***** Abdullah kuwa,koda ya koma Abuja bai rufewa Abbansa komai dangane da halin da Tasleem ta shiga ba. Abba yayi kuka kamar me a karshe yayi nadamar watsi da rayuwar yaransa da yayi wanda sanadin hakan gashi har karuwanci diyarsa wacce ta samu kyakkyawar tarbiyya tayi. Abdullah kuma ya sanarmishi da zancen aurenta da za'ayi da Haris din kamar dai yanda Baffa ya sanarmishi kafin barinsa Kazaure. Abba yaji dadi matuka musamman jin cewar Haris din da kansa ya amince zai rufawa diyarsa asiri yana sonta ba tare da kowa ya tilasta mishi ba. Sannan kuma ya d'okantu da ganin tasleem ko don ya nemi gafararta,amma Abdullah yace mishi ya saurara dai tunda can gidan basu san komai ba. Ya hadashi a waya da baffa ya nuna amincewarsa dari bisa dari ya kuma nunawa Baffa ai tasleem ikonsa ce. Baffa yaji dadi matuka,bayan hakan ne ma ya nemi tasleem yayi maganar gareta. Wannan kenan!! ***** RANAR ASABAR!!!! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (57) Kabir yana zaune a falonshi bayan ya kirayi wayar Momy har zuwa lokacin babu kwakkwarar magana ta inda Baby take. Ya damu kwarai,har abun yana neman shafar walwalarsa. Daidai lokacin Yasmewn ta zauna tana amsa waya cikin dariya ta karashe maganar data soma tun kafin shigowarta da cewa "Aa yayana,mudai kam kada a tsawaita mana lokaci munason shan biki da wuri." Ta danyi shiru a nishadance tana sauraron amsar da Haris ke bata,yayinda KB ya mike zaune yana zuba mata ido cike da dumbin mamaki. "Toh Allah Ya tsare hanya,agaishemana dasu Malam." Daganan ta katse wayar ta ajiye. "Sorry prince,abinci saura kad'an." "Wane yayan naki ne zaiyi aure?" Tayi mamakin tambayarsa,bata dauka koda wasa baisan da zancen ba kuma ganin agabansa aka danyi maganar tafiya kazauren a kano duk da dai ba'a fadada zancen yanda zai fahimta "Baka da labarin sanya ranar auren Yayana za'aje yi Kazaure?" Ransa ya baci jin tambayt daya kalleta matsayin rainin hankali "Da ina da labarin zan tambayeki ne?" Ganin ransa ya baci yasa ta sanyaya murya domin yanzu batason batamishi ko kusa "Kayi hakuri,ganin yanda kuke dashi shiyasa nayi zaton bazaka rasa sanin komai ba. Ni kaina bansan cikakken zancen ba. Amma Daddy ne ya turashi Kazaure zab'ar matar aure cikin yan uwanmu. Kuma yanzu ya zab'a shiyasa Malam ya nemi ganinsu gaba daya harma dasu Daddy din." Kb jikinsa yayi sanyi, me ya yiwa Haris da zafi har haka? Duk irin shakuwarsa amma ya kasa sanar dashi labarin aurensa? Ya jinjina kai kawai baice uffan ba. "Hadomin Coffee." Ta mike ta fita itama din dai ta lura yayan nata saboda abunda KB yayi gareta ne ya kullaceshi wanda ba halinsa bane(wato kullata). Shi kuwa KB wayarsa ya dauka ya kira Haris dake shirin tayarda mota zuwa gidansu Daddy don tafiya. Kamar bazai dauka ba sai kuma ya dauka da sallama. Kb ya amsa yana yar fara'a kafin yace "Wani tsastsauran laifi nayi da har dan uwana kuma aminina ya kasa sanarmin da batun aurensa har haka? Inda aminci kamata yayi ma ace a bakina Princess(yasmeen) zata soma ji ba bakinka ba. Haba Haris,abun har yakai haka? Allah ma munayin laifi gareShi ya gafarta mana ballantana dan adam?" Ya karashe a sanyaye gwanin tausayi domin hakikanin gaskiya KB yana kaunar Haris kwarai dagaske,kauna ce mai tsafta tun suna yara suke yiwa juna. Jin yanda ya narke murya yasa Haris sauka daga fushinsa,shima cikin sanyin murya yace "Dan uwan nawa ne ya kasa saita rayuwarsa,ya kasa fahimtar hatsarurrukan dake cikin sab'awa Ubangiji. Banda wannan babu wani abu dake had'ani dashi." "Oh come on my friend,tuni na watsar da wannan hanyar wallahi. Just ita ke wahaldani ga kuma fama da rashin sanin inda take amma daman banda ita komai na watsar. Ka tayani addu'a." Murmushi Haris yayi na mugunta "Bakomai,itama zaka mantata har abada in sha Allah. Zan tayaka addu'a. Barni hakanan,Daddy suna jirana." "Toh ango,yaya sunan matar.." Kafin ya karasa Haris ya katse kiran yana murmushi "Da sauran lokaci Kb,bazan amince ka rusamin komai ba." Daganan yayi ribas ya fita kasancewar tun shigarsa mota isah ya wangale gate din. ***** Rashin samun wadataccen bacci da kuma matsanancin kukan da baby tasha a daren ya janyo mata ciwon kai matsananci da zazzabi wanda ya sanyata lafkewa saman darduma tun bayan sallatar Asubahi da tayi. Gwaggo Hajara tayi shigowa dakin wajen sau biyar amma bata tashi na gashi har rana tayi sosai domin lokacin wajejan karfe sha daya na rana. Ganin bata da niyyar motsawa ne,yasa Gwaggo tashinta "Wai lafiyarki kuwa 'yar nan? Wane irin bacci kikeyi hakane?" Jin muryar Gwaggo yasa baby bude ido kadan, ganin yanayin baby yasa ta taba wuyanta "Ikon Allah wannan bandejin kuma fa na kanki? Jiya dankwalin kanki bai barni na lura ba,ga jikinki da zafi ashe masassara kikeyi baki fada an nema maki magani ba? Bari na aika kemis din Abdulaziz a amso maki magani. Kokarta ki tashi ki sanya ko kunu a cikin naki." Ta karashe tana kokarin mik'ar da Tasleem zaune,dakyar ta mike tayi azamar rike kanta sakamakon sarawar da yakeyi. Ta daure ta wanko bakinta ta dawo tasha kunun kadan,saidai fa tuni cikinta ya hau murd'awa saida ta ruga bandaki ta amayar dashi tas! Gwaggo na mata sannu. Bayan ta kamota sun fito take fadin "Haba jama'a,ana kokarin yi maki gata amma kina facali da damarki? Harisu yaron arziki ai ba abun gudu bane." Ita dai tasleem batace uffan ba,da gwaggo zata ji labarinta da bata amince da aurawa namiji irin Haris 'Yar Bariki ba. Dakyae ta iya hadiyar magungunan ta sha ruwa sai kuma bacci ya dauketa a saman gadon bayan ta ja bargo ta kudundune jikinta saboda sanyin da takeji yana damunta duk da kasancewar rana ake kwalawa. ****** "Kace ashe harisun sun iso kenan?" Tambayar da taji Gwaggo na yiwa wanda batasan ko wanene ba. Tashinta daga bacci kenan,ba laifi zazzabin ya d'an sauka saidai ciwon kan. Batasam takamaiman karfe nawa ba saida taji muryar Baharu na fadin "Ya iso gwaggo,shiyasa Baffa yace nazo nayi kiranta su gaisa." "Toh ai shikenan,bari na gani ko jikin nata yayi sauki." Jin gwaggo na kokarin shigowa tayi saurin mayarda idanunta ta rufe gabanta na bugu fat fat......! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (58) Ta taba goshinta taji sanyi radau wanda ya tabbatar mata da saukar zazzab'in. A nutse gwaggo ta hau bubbuga kafarta "Tasleem,tasleem." Ta bude ido sannu sannu kamar mai baccin gaske. "Na'am gwaggo." "Sannu ko? Ya jikin naki?" "Alhamdulillah." "Haka nakeson ji,maza daure ki tashi,Baffa ya aiko kiranki ku gaisa da bak'i." Kamar zatayi kuka tace "Banjin dadi fa gwaggo." Gwaggo ta hau lallab'ata "Haba d'iyata,meyasa bazaki kasance mai hakuri a rayuwa ba? Babu amfanin bijirewa maganar manya. Ki tashi kije ai ba auren kikaga anyi ba. Mu dage da addu'ar zab'in Allah." Haka tayita kashe mata jiki da maganganu,Baby ta mike ba don taso ba. "Toh nidai ki sanya a daukomin akwatina sai nayi wanka." Gwaggo tayi dariya "Ai shikenan babu komai d'iyata ta kaina. Shiga kiyi abinki don ma kayana bazasuyi maki ba ai da shi zan baki." Murmushi baby tayi kafin ta soma kwab'e kayan jikinta. **** Ta fito wanka sai kuma ta rasa suturar sanyawa. Manyan kayan daman kala biyar ne. Uku atamfa,biyu kuma shaddoji suma kyautarsu akayi mata. A karshe dole ta dauki daya cikin shaddojin nan ta sanya ba don taso ba. Shaddar brown ce,tasha surfani anyi mata riga fitet hakanan skirt din yayi d'as a jikinta saidai hakan bai boye 'yar ramar da tayi ba. Ta sanya dankwalinta tayi dauri wanda ya rufe bandejin kanta,ta kudurta suna tafiya zataje kemis a fidda mata. Kai kuzo kuga baby acikin hadaddiyar shaddar nan. Batayi kwalliya ba kwata kwata,toh auren da bata murna da yinsa kuma ma me zata nunawa Haris bayan shi d'in daban ne a komai. Ta fesa turaruka masu fisgar hankali wanda har gwaggo dake waje saida tayi mata magana "Kai tasleem,turaren nan kodai na maza ne? Kibar amfani da turare mai k'arfi haka kina mace." Batace komai ba ta maida ta ajiye,ita kam anya zata iya daina shafa turare? Da kamar wuya don ma'abociyar son kamshi ce. Ta zura takalminta sai kuma ta rasa mayafi. Kawai saita janyo na mamma da tun zuwanta take yafawa ta yafashi. Gwaggo Hajara ta dubeta tana zabga murmushi sadda ta fito "Ko babu kwalliya kina da kyawunki diyata ta kaina saidai muje na baki wani mayafi ki sanya wannan ya tsufa da yawa." Murmushi kawai baby tayi gabanta bai bar bugu ba,taji kwallah ta taho mata saidai tayi azamar maidasu. Baharu ya shigo karo na biyu yana sallama ta amsa. Baki ya washe "Antina wallahi kamar bake ba. Kullum k'ara kyau kike." Ta d'an harareshi ya kyalkyale da dariya "Kamar kinsan kuwa surukan naki ne ya tambayeki shine nace bari na turo masa ke." Surukanta? Ta nanata a ranta,ita fa jikinta yana k'ara yin sanyi. Mamaki takeyi ace wai Haris ke sonta,haka kawai tsoronsa yayi mata dirar mikiya. Tunaninta ya katse sa'ilin da gwaggo ta fito rike da wani mayafi kalar ruwan madara(wato surfanin dake jikin shaddar) "Fiddo wannan ki yafa wannan." "Kai gwaggo ashe kinsan kalar gayu." Cewar Baharu. Baby dai kamar kurma ko don bata fiye son yawan magana bane? Oho. Amma batace musu uffan sai murmushi na dole. Suka jera Baharu yana bata labarin yanda surukan suka yaba da wannan auren ji sukeyi tamkar a daura auren ma a yau. "Wallahi anti angon nan naki burgeni yakeyi kana ganinsa kaga dan boko kuma wayayye amma ko kusa bashi da wulakanci ko girman kai. Kunyi bala'in dacewa dashi wallahi." Ta dubi Baharu zatayi magana ta fasa sakamakon ido hudu da sukayi da Haris ya fito yana amsa waya. Sanye da manyan kaya amma babu babbar riga, kansa sanye da hula. Sai taga yayi mata kyau da kwarjini sosai,shi kansa Baharu saida yaga yayi mishi kwarjinin. Ya daure fuska yana mai kauda kansa yana mai juya musu baya ya cigaba da wayarsa da alama dai da kanwarsa yakeyi. Ta sunkuyar da kanta yayinda kwallah suka cika mata idanuwa. Daman tasan ba sonta yakeyi ba. Har suka is a daf dashi bai bar wayar ba hakan yasa tayi cikin gidan,zata karasa can wajensu inna,Baharu ya dakatar da ita da cewa "Ki soma shiga suna nan d'akin fa anti." Ta gyada kai kawai,gabanta na faduwa tayi sallama. Dukkansu suka amsa kafin ta shiga kanta yana k'asa. Su kuwa su Abba ganin surukar tasu nan da nan fara'arsu ta k'aru bare ma Malam Hussein wanda yaji tamkar diyarsa ce. Ta gaishesu a ladabce,suka amsa kafin ta tambayesu hanya. A karshe Malam Hussein ya kara jin ta bakinta sannan yazo mata da batun cewar ba ita kadai Harisu zai aura ba(kamar yanda suka zauna sukayi zancen da yaransa abba da daddy da hajja kubra,Haris ya amince da hakan ga mamakinsu. Itama Zahra tayi na'am tana mai farinciki saboda son da takeyiwa Haris mai girma ne.),hankalinta ya tashi jin wannan zancen. Saidai ta daure tunawa da nasihar gwaggo tace ta amince da bakinta. A karshe suka sanya mata albarka ta mike ta fito kanta na k'asa suna zubar hawaye. Jikinta kuwa rawa yakeyi gabanta na dukan tara tara sakamakon tunanin daya darsu a zuciyarta na cewar lallai d'osanawa Haris ita akayi,daman Zahra yakeso. Tana kokarin sanya takalminta amma jikinta rawa yakeyi,ta dunguro zata fad'i tayi azamar kai hannu da niyyar dafe bango saidai taji ta dafa hannun mutum. Da sauri ta dago idanunta ya sauka akan kyakkyawar fuskarsa,taja baya bayan ta sakeshi. "Sorry." Ta furta murya na rawa,ya matso saitin kunnenta ya soma magana "Kina tsammanin sonki yasa na amince zan aureki ne Tasleem? No! Lik'amin ke akayi,ni kuma babu yanda na iya na kaucewa maganar magabatana. Zahra itace zab'ina! Abar kaunata! Zan aureki bisa kaddara kawai!" Ta juyo da sauri, ganin numfashinsu na gogar juna tayi azamar ja da baya tana kallon fuskarsa,murmushin mugunta kawai yakeyi mata a zahirin gaskiya kuwa daurewa kawai yayi domin cin zarafin dan adam baya daga d'abi'arsa. Ya daga mata gira yana murmushi "Idan kinga zaki iya,muje zuwa toh..." Daga haka ya wuceta ya fita ya fasa shiga dakin ma. Kawai tayi ciki a guje takalmin da bata sanyaba kenan...!! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (60) Takai mintuna biyar kafin ta kammala saidai kuma jin yanda hayaniya da shewar murna ta cika dakin inna ya hana Tasleem fitowa yayin data kifa goshinta jikin kofar bandakin tana rusar kuka. Ta tabbata an daura aurenta da Haris akan sadaki dubu hamsin. Shikenan Haris ya samu damar wulakantata da cin zarafinta. Yan uwanta sun kasa fahimtar Haris ba kaunarta yakeyi ba. Ta bandakin tana jiyo muryar Baharu yana labarta musu cewar ai Haris ne ya nemi a daura auren a yanzu,Abba(alhaji Aliyu,mahaifinsa) yana fadan wane irin gaggawa ne haka? Liman yace hakan shine daidai tunda gashi an hadu domin har mijin Mamma,Dad yana wajen wanda shine ya zama wakilin tasleem aka daura auren kawai. Zahra ma an daura saidai an bar tarewar sai nan da wata daya bayan an kammala shirye shirye. Nan dakin ya dauki kabbara cike da sowar farin cikin jin wannan labari. Tana jin sadda d'iyar Dada(dada matar kanin Liman daya rasu take zaune gidan) wacce take zawarci sakamakon mijinta daya rasu da jimawa,wato Hafsa ta tahowa tana buga kofar tana fadin "Fito kin kunshe kanki a bandaki,komin abunki fa sai mun murjeki da lalle." Aka kwashe da dariya kafin dai kowa ya tattara ya fice. Saida taji shiru sannan ta fito, ji tayi an rukunkumeta ana dariya "Ja'ira,ai daman nace sai na ga fuskarki." Cewar Hafsat. Tasleem tana kuka tace "Anti Hafsa kina kallo aka auramin wanda baya kaunata baya sona? Anya ba'a kwareni ba?" Jikin Hafsa yayi sanyi,ta ja hannunta suka zauna bakin gado "Haba Tasleem,kinga yanda yake rawar kafa da wasa da dariya kuwa? Anya zan amince baya sonki? Kodai kece bakya sonshi ne?" Tasleem tayi shiru da kukan,toh tana da bakin cewa batason mutumin da tun zuwanta Kazaure dashi take kwana take tashi a zuciyarta? Tabbas tana son Haris. Banda Rilwan bata taba son wani d'a namiji ba da zuciya daya sai shi. "Kinyi shiru?" Inna dake jinsu tace "Ki rabu da wannan sakaryar wacce batasan abunda ya dace gareta ba. Nikam takaicinta ma yana sanyani jin kamar na kwasheta da mari." Hafsa taja hannun Tasleem sukayi hanyar fita zuwa dakinta tana fadin "Ayi hakuri innarmu,kinsan sabon shiga." Inna ta tabe baki suka nufi dakin Hafsat. Ita dinma rarrashi da ban baki gami da gwada mata hanyoyin kissosi da zata bi domin mallakar zuciyar Haris cikin sauki. Tasleem dai sauraronta kawai takeyi,wannan ba matsalarta bace,babu wani abu na fannin kissa da bata kware dashi ba saidai Hafsa ta gaza fahimtar matsalarta. Ita fa kalaman da Haris keyi mata ne yake daukar hankalinta. "Nan zuwa sati biyu za'a kawo lefenku. Aurensa dake aka soma d'aurawa sannan kuma da Zahra. Kinga kenan matsayinki ta babba dole saikinyi hakuri kin rike girmanki koda dai Zahra bata da raini yarinyar akwai hankali da nutsuwa ba kamar su Atika ba. Duk da haka sai kin dage." Haka dai sukayita hirarsu har Hafsat take bata labarin zaman hakurin da tayi da facalolinta wanda yasa Tasleem sakewa sosai. Sallamar Musty ta katsesu. Ya shigo suka hada ido da Tasleem yayi mata murmushi a sanyaye "Babana ya akayi?" Cewar anti Hafsa kasancewar sunan kanin Liman yaci kuma mahaifi gareta. Hakanan mustapha jikan Dada ne mahaifiyarta sannan shi din maraya ne gaba da baya a hannun Dada ya girma har zuwa aurensa da Farida. Ya zauna saman hannun kujera yana yamutsa fuska "Ina fa lafiya kuna ji kuna gani an kwacemin matata." Duk suka dubeshi Tasleem kuwa saita dauki abun wasa ashe Antin ma wasa ta dauka jin tayi dariya tace "Me zatayi dakai yarinya yar birni.?" Ta fice daga dakin,Tasleem ta gaidashi yak'i amsawa "Small ashe zaki iya auren wani ba ni ba?" A mamakince ta yamutsa fuska kadan kamar bazatayi magana ba sai kuma tayita tamkar bataso "Wai daman kana sona ne yaya?" Musty ya ciji lebbansa cike da takaici "Tun kina secondary nake dawainiya da sonki. Allah bai kaddaro ke zam fara aure ba sai Farida. Yanzu kuma gashi ina murnar dama tazo min sai kawai na tsinci labarin aurenki da wannan gayen." Ya danyi shiru itama tausayinsa takeji, "Haka Allah Ya kaddaromin. Allah Ya baki zaman lafiya da mijinki. Saidai ina fushi har yau gashi satinki daya cif a garin nan baki tako kinga matata ba shiyasa nima duk da dokin ganinki da takeyi domin ina yawan bata labarin sister dita mai sona amma na hanata zuwa." Ya karashe a wasance,itama ta share wancan zancen watakila dai ya tuna a yanzun matar aure ce, "Kayi hakuri dai yaya mustyna,zan shigo." "Ai na mantaa yanzun saida iznin oganki ko?" Gabanta ya fadi,ashe yanzu komai zatayi saida iznin Haris? Tab ai kuwa ta gwammace tayi ta zaman gidan gashi tana matukar son komawa wajen mahaifiyarta domin ta kara neman afuwarta. "Bari na wuce." Ya maidota daga kogin tunanin data shiga,ta dubeshi har yakai kofa "Toh yaya saida safe." Itama ta mike ta koma dakin inna. Sallar isha'i kawai tayi kafin tayi zaman hira da inna. Sai ga Liman ya aiko kiranta. Ta iskeshi babu kowa a dakin sai shi. Nan yayi mata doguwar nasiha akan aure da nuna mata ita din yanzu fa karkashin ikon Haris take sannan ya gargadeta data dunga mutunta shigarta. A karshe ya damka mata sadakinta tace ita yanzu bata da abunda zatayi dashi,ya adana mata. Yace shikenan. Ta mike ta fita, zatayi ciki taji muryar Baharu a bayanta yana kiranta dole ta tsaya ta dubeshi ta lura dai d'asawa yakeyi da Haris sosai. Leda ya mik'omata yana dariya "Gashi inji maigidanki." Ita kam duk sadda aka dangantata da Haris sai gabanta ya fadi,tasa hannu ta karba babu ko godiya tayi ciki. Waya ce da chajinta da komai,sai kwalinta da alama harda sim. Blackberry ce. Sai kayan ciye ciye, nan inna ta hau duddubasu tana fadin oh,abun dadi basu karewa a duniya. Wayar tayi k'arar shigowar sak'o. Ta bude ganin lamba. "Ga waya nan,ban amince ki bawa kowane namiji damar mallakarta ba ke daidai da dan uwanki banda Abdullah banason ganin lambar kowaye! "Harith" Ta tabe baki ai shi d'inma bazaici darajar saving number nasa ba a wayar. Ta ajiye wayar ta mike domin watsawa kanta ruwa haka dai inna ta dauka tayita kalle kallenta tana fadin yanda wayar ta burgeta kwarai. 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (59) Cikin fushi inna ta ture tasleem daga jikinta "Ke ni matsamin kibani wuri shashashar banza kawai! Aure hauka ne? Don za'ayi maki gata ke kuma kin kasa fahimta? Toh wallahi ba baki zanyi maki ba Tasleem,amma matukar kika bari batun auren nan naku ya rushe da yaron nan zaiyi wuya ki samu madadinsa. Ke kamar wata yarinya karama,a hakan ake cewa kinyi degree? Amma tabbas bakiyi kama da matan jami'a ba sam sam baki da wayewa. Mts. (Hhhh kuji fa! Baby ake fadawa duniya..cewar Rufaidarh) Ta dago ta dubi inna dake faman zazzaga masifa "Shi da bakinsa fa yace baya sona lik'a mi.." "Kina nufin Liman k'arya yayi maki?" Ita dai batace uffan ba,ai sai fadan inna ya k'aru karshe tace bazata iya ba saita had'ata da mamma. Sai kuma tayi shiru kafin ta kara cewa "Allah Ya kyauta,namanta ashe ita dinma daren jiya tazo tana surutanta wai don me za'a yiwa Harisu haka? Saida na zageta tsaf na nuna mata kurenta sannan tace shikenan. Haka kawai kunbi kun tsani yaro na arziki ma." Haka dai inna ta mike ta fice bayan ta dauki furar data kammala damunsa zata bayar a mik'awa bak'i. Baby ringingine ta kwanta ta lumshe ido yayinda kwakwalwarta ke k'ara tunano mata bakaken maganganun Haris daya jefa mata. Zarginta ya tabbata kenan ba sonta yakeyi ba? Zahra,Zahra? Wacece ma hakan? 'Yar farar yarinyar nan dai siririya mai siririyar fuska. Kallo daya zakayi musu ita da Haris ka tabbatar da cewar jini d'aya suke saboda matukar d'ibar kamar da sukeyi da juna. Bata da mazauna sosai hakanan kirjinta baida cika sosai. Tabbas ta tuno Zahra, itace dai wacce tayi mata rakiya gidansu KB. Murmushi kawai tasleem tayi tunawa da sanyin halinta. Babu ruwanta watakila shine dalilin da yasa Haris ke sonta. Kaico da rayuwarta,ita kam ba abun ta samu su Baffa ba tace bata kaunar auren nan. "Taso kije Harisu ya aiko kiranki." Ta bude idanuwanta sosai jin muryar inna. A sanyaye ta mike,ita fa batasan dalilin da yasa take shakkar Haris ba,kai bata taba kawowa bama zataji tsoron wani d'a namiji ba sai Haris. "Don Allah ki mutuntashi babu kyau wulakanta mutum." Murmushi tayi mai ciwo,ta mike ta dauki mayafinta ta fita bayan ta zura silifas. Ta nufi zauren saidai bayanan,ta karasa waje gabanta na dukan tara tara. Hon da taji ya tabbatar mata cikin motarsa yake, hakan yasa ta karasa kafin ta bude ta shiga. Bazata mance motar nan ba a tarihin rayuwarta,motar data fayyacewa Haris komai na sirrin rayuwarta? "Baki iya gaisuwa bane ko kuwa dai rashin tarbiyya zaki gwadamin?" Ta kalleshi "Haris wai menayi maka hakane? Haris ka chanja ba haka...." Kallon daya watsa mata shi ya sanyata yin shiru. "Ba wannan na tambayeki malama." "Barka da yamma." Ya tabe baki kadan "Rike abinki tunda rok'a nayi. Abunda nakeson sani shine,kinga period naki?" Ta kauda kanta ga barin kallonsa "Da asuba nayi wanka." "Kina iya tafiya." Shiru na mintuna,ganin bata da niyyar motsawa yasa shi saurin fita ya rabu da ita a motar. Tana kallonsa ya koma ciki,hawayenta suka kara kwaranyowa karo na ba adadi,toh zaman me takeyi kuma? Kawai saita bude ta fito itama. ***** "Ayyiriri yiriri! Kai Alhamdulillah. Harda na Zahra?" Batasan lokacin da cikinta ya murd'a ba,me kunnuwanta ke shirin ji mata ne? Innalillahi wa inna ilaihiraaji'un! Da azama ta nufi bandaki domin rage cikinta......! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar (61) Washegari wajejan uku na rana,mutan gidan basunan sunje gaisuwa acan k'asa gidan wani almajirin Liman wanda ya rasu sakamakon hatsari. Tasleem ce zaune a tsakar gidan cike da tunanin kawayenta. Tunani takeyi ko Manal tayi aure? Toh Dalal da Hibba fa ya suke? Tunanin neman layin Hibba ya fadomata. Bata mantawa saboda saukin lambar wayar Hibba ta haddaceta a kwanyarta har akwai ranar data taba karantowa sukayita mamaki har hibbar domin ko ita bata da haddar lambarta aka. Da azama ta mike tayi daki,wayar dai data tsana ita ta dauko ta dawo ta zauna. Ta duba akwai kud'i har dubu daya a ciki. Baki ta tab'e wannan kam a wurinta karamin kudi ne bazai burgeta ba. Batason wulakanci a rayuwa. A nutse ta jera lambar ta kira. Akayi sa'a ta hau ringing. Hibba alokacin tana zaune a gefan ruwan Tiga Dam ita fa sabon saurayinya,HAYAT. Tunda ta soma bariki bata taba tsintar kanta dumu dumu cikin soyayyar wani d'a namiji ba illah Hayat. Matashi mai ji da naira da hutu. Ganin unknown number yasa ta jan tsaki ta ajiye wayar. Hayat ya dafa cinyarta yana kasheta da kallon kauna "Lafiya dai my beb." "Wata number ce da bansan da zamanta ba." Acan kuwa baby tsaki taja sai lokacin ta tuna ko ita akayi kira da unknown no.a wayarta bata fiye dauka ba. Ta yanke shawarar tura sak'o. "Hibba,it's me Baby. Pick d call." Tana shirin turawa yayi sallama ya sanyo kai. Ta amsa bayan tayi saurin ajiye wayar a gefe. Hankalinsa yayi kan wayar cike da zargi kafin ya basar ta hanyar fad'in "Ina mutan gidan?" Itama fuskarta ba yabo ba fallasa saidai kirjinta sai bugu yakeyi. "Basunan sunje gidan gaisuwa." Bata ankara ba taga yasa hannu ya dauki wayar yayi tsai yana karanta sak'on.... 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (62) Fuskarta a tamke baisan sadda ya daga wayar ya bugata da bango ba kafin ya fisgo Tasleem wacce ta mike tsaye ganin yanda ya yiwa wayar. Murde hannunta tayi ya komar dashi ta bayanta,har suna shakar numfashin juna ita kam na tsoro ne. Tayi ta murza hannun saidai fa iyaka yatsunta ne don kuwa ba rikon wasa ta samu daga wajen maza ba. Cikin kakkausar muryar da batasan Haris da ita ba yace "Menene gaminki da ita a karo na biyu?! Me kike shirin yimin? Daga yau ki sani cewa banason mu'amalarki da kowace abokiyar shaidancinki ta baya! Wannan shine gargadina a gareki na karshe." Daga haka ya saki hannunta,tayi saurin ja baya tana zubar hawaye. Ta dubeshi ido cikin ido kallon nan na alamar tambaya(Kaine kuwa?..lol). Ya kauda fuskarsa,har ya juya zai fita kuma ya dawo baya ya dauki wayar wacce tuni screenface dinta ya tsage,sim d'in ya fidda kafin ya cilla wayar jikinta daga haka yayi gaba cikin takunsa kamar wani basarake. Ta dubi hannunta wanda har yatsun Haris sun bayyana jikinsa,kafin ta lumshe ido ta zauna d'abas akan sumintin tsakar gidan tana kuka. Karshe dai mikewa tayi ta dauki wayar tayi daki. Jimawa kadan taji sallamar Baharu,bata ko fito ba har ya shigo ya miko mata simcard sabo. "Gashi inji angonki,yanzun nan suka wuce. Yace ki sanya a wayarki zai kiraki." Bata ko kalleshi ba ballantana yasa ran zata karb'a,ganin shiru ya ajiye ya fita yana mai jin haushin yanda antin nan tasa ta kasa gano kaunar da Haris keyi mata. ***** Tsaye yake a farfajiyar hotel din na Nicon dake birnin tarayyar Abuja yayinda yake cike da farin ciki da walwala na ganin wacce bai taba tsammatar ganinta ba a wannan lokacin. Ta karaso bayan ta cewa wacce suke tare tayi jiranta minti biyu. Ta wulka ido irin na kwararrun 'YAR BARIKI kafin ta sakar mishi murmushi wanda ya kara fiddo zahirin kyawunta na asalinta na buzuwa. "KB manya daman ana ganinku?" Kb yayi yar dariya "Gaisheki DALAL,kun b'ata b'at a garin ta dabo. Ashe kina nan kina holewarki." Dalal tayi dariya "Kai haba,mu a suwa? Kaine dai gakanan sai fresh kakeyi,nikam tunda mun hadu yau bazan bari ka gudu ba saika kaini na gaisa da k'awarmu. Wallahi just one week kenan da bamu ganta ba amma kewarta ta cikamu." Cikin rashin fahimta yace "Wai Dalal kuna zaton Baby tana tare dani ne?" Tayi k'as k'as da cingam tana kallonsa shek'ek'e "Bangane manufarka ba KB? Wai bakwa tare da Baby? Toh ina take?" Yayi wani d'an malalacin murmushi kafin ya zura hannu aljihun wandon jeans nasa. 'Yan dubu dubu ne da baisan ko nawa bane ya zaro da d'an kaurinsu ya mik'a mata "Idan basu isheki ba kiyi magana na k'ara maki Dalal,fatana da burina bai wuce ki taimaka wajen lalubomin inda kawarku take ba. Ko kuma idan kinsan wani labari game da rayuwarta please ki sanarmin sauran binciken zanyi da kaina." Ta shinshina kud'in,ita kam ai kud'i koyaushe basu tsufa awajenta sabbi ne. Ta tura a jakarta bayan ta tuno da Manal data tab'a tabbatar mata cewar ita kadai tasan wacece baby da kuma garinsu saidai bisa amana ta gayamata ita kam bazata fadawa kowa ba. "Aikinka zai cika muddin zaka saki kud'i Hajy KB." Shima kallo yakeyi mata na kwararren 'Dan Bariki,kafin ya shafi sumarsa yana dariya "Ba abune mai wuya ba,kina iya bani acc.no dinki hade da phone.no." Ya amsa kafin suyi sallama ya shige don gabatar da abunda ya kawoshi cike da matsanancin farin ciki....! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (63) A gajiye ta k'arasa kujerar tangameman falon wanda yaji kayan alatu ta zauna tana fadin wash! Manal ta zube gefanta suna dariya "Shegiya Dalal,kina cin karenki babu babbaka nikam ina nan kamar kullin kayan wanki. Ke a yanda na lura anya kuwa Alhaji Ubalen nan idan munyi aure zai barni na fita wani wajen? Mahaukacin kishi gareshi,ji fa dai daga maganar aure har ya killaceni gidansa,babu wata harka wai yana bukatar nayi istibra'i,mts." Dalal ta mike zaune tana dubanta bayan ta kyalkyale da dariya "Kefa baki fahimci wannan d'an fulanin naki ba,toh wallahi dagaske yakeyi sonki yakeyi da gasken gaske." Ta tabe baki "Barshi dai yayita haukansa,wani sa'in ni kaina ina jin kauna da tausayinsa wallahi ya iya lallab'a mace ne. Ke nasa fa an bincikamin asalin aurensa da matarsa,ashe dole yabi umarnin mahaifinsa ya aureta har yanzu da suke da yara biyar bai taba sonta ba. Kinsan fa ba wani shekaru ne dashi ba,arba'in da wani abu yake." "Yara biyar? Kuma ace ba soyayya? A ruwa tasha?" Manal ta harareta da alama maganar ta bata ranta,Dalal kam murmushi tayi gami da jin tsoron auren wata uku ya koma na har abada.... "Wai kuwa kina samun Baby a waya? Nasha nemanta naji switched off." Jin an ambaci Baby ya tunasar da Dalal abunda ya kawota. Ta zabura ta matso kusa da Manal har tana firgitata. "Ke nima bansan inda ta lulluk'a ba,anya ba garinsu ta koma ba?" Manal tayi shiru tana tunani,daman tun sadda baby ta fito da shigar hausawa jikinta ya bata cewar Kazaure zataje. "Gayamin sunan garinsu mana,kinga sai na gano mana ko lafiya?" Cewar Dalal,Manal ta numfasa "Banason karya alk'awarin dana daukarwa baby na cewar bazan sanarwa kowa ba game da garinta ko asalinta,wannan shine..." "Haba Manal, bamusan halin da take ciki ba,idan ance ma tana bukatar taimako babu k'arya a ciki. Idan kin fadamin wa zan gayawa,just give me full address ni kuma zan binciko mana lafiyarta koda a b'oye ne. Kinga idan bata garin sai mu sanya cigiyarta ko kuma mu bi abokan harkarta gaba daya tunda ba wani yawa garesu ba muji ko suna tare." Manal tace "KB fa?" "Basu tare da KB,domin kuwa Momy tace min yazo nemanta wajenta amma bai sameta ba." Dalal tayita siyasance Manal har saida ta samu ta shawo kanta tayi na'am da hakan batare data bata ko sisin naira biyar ba. Duk da dai Manal bata da tabbacin baby can tayi amma bata zaton zata je gidan yayanta da mahaifinta domin a yanda ta nunawa Manal ba karamin tsana tayi musu ba,mammanta ce ma take son sanyata ido wataran. Ta gayamata ta rubuta. "Idan kinje Kazaure ki nemi gidan babban limamin garin, nan ne gidan da nasan watakila ki samu labarin Baby." Bayan ta gama rubutawa,Dalal ta tuntsire da dariya "Amma Baby anyi shegiyar yarinya. Don ubanta ita daman d'iyar Liman ce take bura uba haka?" Manal ma dariyar tayi,saidai tsoron kada Baby ta kamata da cin amanarta yasa bata gayawa Dalal cewar gidan kakannin baby ne ba ta wajen mahaifiyarta. Da zataji waye uban baby,zata fahimci cewar lallai Baby ta ketaresu kota ina tunda ba kudi ne ya fiddota bariki ba. ****** Kishingide yake a kujera mai zaman mutum uku,Yasmeen tana gefe tana mammatsa mishi kafafuwa yayinda ya maida hankalinsa ga kallon Ball. Wayarsa tayi k'arar shigowar sak'o "Mikomin wayata." Ya fada ba tare daya dauke idanunsa daga kallon ba. Ta dauki wayar ta mik'a masa. Ganin sak'on daga Dalal ne,ya sanyashi mikewa zaune. "Kazaure gidan babban Liman,duk wanda ka tambaya za'a kaika. Idan kaje babu nasara zan k'ara bincika mana." "Wuuu!" Shine ihun murnar da KB ya saki. Yasmeen ta iso gareshi "Lafiya prince?" Ya mike ya dagata sama yana juyi da ita suna dariya. Babu kamar Yasmeen wacce take jin mamakinsa da kuma farin ciki. Yaushr rabon daya kula da lamarinta haka? Kai a ranar dai ya faranta mata fiye da tsammaninta. Shi kuwa Allah Allah yakeyi weekend yayi yaje ga Baby shi koda bai ganta bama ya samu shiga wajen liman. Domin kuwa yasan kwarai wanene Liman saidai bai taba kawowa shine uban tasleem ba. Har ya soma mamakin abunda zaisa Tasleem wacce ta fito gidan manya haka ta b'ata rayuwarta da barikanci. Meyayi zafi haka toh? ****** Karshen sati nayi,ya yiwa matarsa sallama da sunan zaije Kazaure gaida kakanninsu. Taso ya tafi da ita saidai koda ta matsa da magiya ya bata rai a dolenta ta hakura tana ji tana gani yayi mata sallama ya wuce airport domin hawa jirgin zuwa Kano. Tunawa da tayi cewar tun angoncewar yayanta bai nemeta a waya ba yasa tayi kiransa. Yana dauka ta soma shagwaba murya "Haba yayana ashe daman akwai sadda zaka share lamurana? Nikam har na soma fushi da yayyuna nasan waya dasu ya janyo ka shareni." Haris dake kwance akan gado kawai yana hutawa domin ya jima da tashi daga bacci,darem jiya sun sha waya da Zahra wacce babu laifi ta samu gurbi sosai a zuciyarsa duk da dai karfin hirar itace shi kam yakan rasa abun cewa saidai ta jefo mishi tambaya. "Kiyi hakuri small,ban manta dake ba. Ai babu matar da zata mantar dani ke. Ya kuke? Ya dotana?" Yasmeen tayi dariya "Gatanan tana tsalle tsallenta,babanta ma yanzu ya tafi Airport zai wuce Kazaure idan ya sauka anan Kano. Wallahi naso ya taho dani naga amare amma yak'i." Tunda Haris yaji wai KB ya taho Kano zaije Kazaure yaji bacin rai matuka ya dirar masa. Bazai fa amince da wannan sakarcin ba,ya dace tun yanzu ya sanyawa lamarin burki. "Hello." Cewar Yasmeen jin yayi shiru. "Small,bani mintuna." Ya katse kiran ya mike zaune yana mai zuro kafafunsa k'asa. Dabara ce ta fadomishi na kiran Mamma. Matar da tunda ta ganshi ta nuna mishi kauna hakanan sun jima a falonta su biyu suna tattaunawa game da Tasleem sannan ya nuna mata komai dangane da lamarinta ya sani. Har kwallah tayi don farin cikin jin cewar yaji ya gani yana son diyarta zai iya aura. Bayan sun gaisa yace yanason Nura yaje ya dauko Tasleem a mota harda kayanta ta zauna a wajenta. Mamma ta tambaya ko lafiya. Bai sanar mata ba saidai yace akwai 'yar matsala ne. Tace bakomai zatayi hakan. Tasleem tayi mamakin ganin Nura yazo wai Mamma da kanta ta nemi komawarta gidanta. Har inna tana fada wai Mamma babu ko kara,bata tambayi ko da iznin Haris ba ko Aa saboda taji Nura yace shine yayi kira. Hakanan ta hau mota,Nura yaja suka nufi gidan Mamma sai tambaya takeyi Mamma da fara'a tayi maganar zuwanta ko a'a shidai Nura tun yana amsawa har tambayoyin sukayita bashi dariya ma. ****** KB yana dira a Kano,direbansa ya kaishi gida. A gaggauce yaci abinci yayi wanka sannan ya saka kananun kaya. Jakar kayansa ya dauka ya saka a mota. Jeep dinsa ya dauki yayi hon Maigadi ya bude.. Sai Kazaure......! 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (64) Hankalin Haris bai kwanta ba har saidai ya lalubi layin baby saidai baiyi mamakin jinsa a kashe ba yasan tayi fushi tak'i sanyawa ne. Wannan yasa ya k'ara nemanta ta hanyar layin Mamma. Ya sanarwa Mamma yanason magana da baby. Ta mik'awa Tasleem lokacin tana zaune anan gefen Mamma suna 'yar hira don babu laifi ta sakarmata. "Sai ki tashi ki shiga daga ciki mijinki ne." Ta mike ba don taso ba wayar na hannunta. Saida ta zauna gefen gado sannan tayi mishi sallama. Ya amsa ciki ciki "Kina jina ko? Kb yana hanyarsa ta Kazaure." Tabe baki tayi,ai daman tasan ko ba dade ko ba jima sai KB ya samu labarin inda take tunda har yasha alwashin nemanta ruwa a jallo. "Ya akayi yasan da zamanki a Kazaure?" (Ya fadi hakan da niyyar bugar cikinta duk da bashi da tabbacin saboda ita Kb zaije Kzu.) Cikin rashin fahimta tace "Kana zargina ne da gayawa KB inda nake Haris? Ko ka mance garinsu ne?" Ya lumshe ido ya kara gyara zaman towel din dake daure a kugunsa,fitowarsa kenan daga wanka. Zak'in muryarta daban ce,hakika zai iya rantsewa bai taba sauraron muryar mace a fili ko waya ba, da yayi mishi dadi irin na Tasleem. "Nidai ina mai gargadinki,stay away from him. Kada koda wasa na samu labarin kun hadu har maganar fatar baki ta shiga tsakaninku. OK?" Ta rausayar da ido tana tsuke baki cikin jin haushin Haris. Banda abunsa ma,kare ne ya cijeta da zata k'ara waiwayar BARIKI. Don KB barikin ne ma gaba daya a rayuwarta. "Kin rasa baki ne?" "Naji zan kiyaye." "Good,had'ani da Mammana." "Ko a ina ta zama taka?" Ta fadi a zuci,a fili kuwa da toh ta amsa kafin ta mike ta fita zuwa falon. Mamma ta karbi wayar,sunyi magana wacce Tasleem batasan abunda yace mata ba saidai ta lura da hararar da Mamma ta dafko mata kafin ta amsawa Haris da cewa "Kada ka damu d'ana,baza'a samu wata matsala ba." Daga haka ta kashe wayar ta mike tayi dakinta a fusace. Wannan ya sanyayarwa da Taslewm da jiki ta mike ta rufa mata baya. Kuka sosai ta tarar Mamma nayi. Ganin ta shigo ta zauna Mamma ta ja majina "Kin cuceni Tasleem. Idan na tuno kinyi karuwanci raina baci yakeyi naji ke kanki ina jin haushinki. Wallahi koda wasa naji kin sab'awa mijinki babu ni babu ke. Ba don Liman ne da kansa yazomin da batun aurenki da yaron mutuncin nan ba wallahi ban yarda a cuci rayuwarsa a aura mishi ke." Jin haka itama Baby ta fashe da kuka sosai ta durkusa gaban Mamma "Wannan ya nuna har wannan lokacin baki yafemin ba Mamma. Ya kikeso nayi,Mamma idan bada sanya albarkarki gareni ba komai na rayuwata bazata tafi a daidai ba. Please Mamma kada kiyimin bakin da zan kasa zaman aure." Jin wannan furucin ne ya tashi hankalin Mamma,ta rungumo diyarta tana fadin "Na yafemaki Tasleem,bazaki fi haka lalacewa ba. Har abada in sha Allah kin shiryu kenan,bana fiddaki a addu'ata." Farin ciki yasa Tasleem dariya. Mamma ta kara dubanta bayan ta saketa "Kabiru da Harisu sun taba ganinki cikin waccan rayuwar,hakan yasa Harisu rokona akan kada na bari ki hadu dashi." Ranta idan yayi dubu ya baci,Haris yafison kare sirrin abokinsa akan nata?? 'YAR BARIKI ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers) (65) Bata cewa Mamma komai ba banda toh. ****** Yaran gida sai ihun murna sukeyi da ganin Kabir. Hajiya Atine ce a tsakar gidan zaune kan tabarma suna hira da mai musu hidimar girki yayinda take kwasar tuwo. Ganin dagaske jikan nasu ne ta hangame baki tana dariya "Ashe da gaskiyar yaran nan. Lale marhabin da mijin." Kabir yayi dariya suka gaisa suka taba barkwanci kafin ya shige wajen kakarsa Hajiya Badi'at. Itama karatun Kur'ani takeyi,sanye da gilashinta na ciwon ido,ganin Kabir ta karashe aya tayi addu'a kafin ta shafa. "Ashe zakazo nan kusa? Ai da bamu ganka tare dasu Harisu ba nayi zaton kaida zuwa nan sai biki kuma?" Ya kai hannu ya bude firij ya dauki robar ruwan Faro,yana kokarin budewa yayi dariya "Haba dai? Ai dole nazo ganin amaren namu. Ko Haris din baisan da zuwana ba so nakeyi dai na bashi mamaki. Wai ma naga kokarin Haris,naji don karfin hali mata biyu ya aura? Yayi kokari." Ya karashe yana mai daga robar ruwan ya soma kwankwada. Hajiya badi'at tayi dariya "Kai don bakaga zuk'ak'an matan da ya zab'a ba. Zahra da Tasleem,....." Tuni ya maido ruwan bakinsa ya fesar har yana b'ata jikin Hajiya Badi'at. Ya cigana da tari saboda ba karamin kwarewa yayi ba. "Baka da hankali ne? Kana shan ruwa kamar wani karamin yaro? Ji yanda ka b'atamu?" Hankalinsa baya tattare da ita,gabansa na bugu da sauri da sauri. Ganin yanda gaba daya ya chanja yasa Hajiya Badi'at dakatawa tana k'ara cillaro mishi idanuwanta wadanda tsufa ya soma tab'awa. "Kai Kabiru lafiya kake?" "Hajiya wacece Tasleem da Haris ya aure ne?" Ta d'an tabe baki "Kai amma Allah Ya kyauta,ai na dauka wani abun ne wallahi. 'Yar wajen maryama ce ta gidan Liman." "What?!!" Ya fada cikin tsawa wanda ya tsorata 'yar tsohuwa Hajiya. Ya mike tsaye,duk jikinsa rawa yake. Nan da nan idanunsa suka kad'a wai kodai wata ce daban? Da sauri ya fito daga dakin ya zura takalmansa,yana ji Hajiya na kwala mishi kira amma baijin yana cikin hayyacin da zai samu ya tsaya. Bai dire ko'ina ba sai gidan Liman. Tsayawa yayi ya rasa ya zaiyi,gashi ba wani sabo yayi da mutanen gidan ba saidai ko ta halin k'ak'a yau sai yaga Tasleem matar Haris. Yana nan tsaye yana shawarar shiga ko tsayawa anan,saiga Baharu ya sauka saman mashin dinsa yana kokarin tsayar dashi. Kb ya karasa wajenshi sukayi musabaha,cikin sakin fuska kasancewar Baharu yasan Kb. "Yaya kabir saukar yaushe?" Kabir yayi murmushi wanda iyakarsa lebbansa "Dazun nan na sauka. Ina amaryarmu?" Baharu ya washe baki yana dariya "Anti Tasleem tana nan mun b'oye maku ita har sai ranar." Kb ya share wannan don ba shine a gabansa ba. "Kana iya yimin magana da ita? Sak'o angon nata ya bani." "Kash,ai kuwa tana gidan Mammanta." "Ko zan samu rakiyarka gidan?" Ba musu suka hau mashin din Baharu suka tafi. KB burinsa yaga wacece Tasleem matar Haris,baya fatan ta kasance bebinsa. Haka har suka iso kofar tangameman gidan. Kb yabi gidan da kallo kafin ya tabe baki "Not bad." Ya fadi a zuci. "Bismillah shigo." Ya bi bayan Baharu suka shiga. A nan tsakar gidan suka iske Humaira gwaggo mai aikin Mamma tana turata a saman kekenta. Kuri KB yayi mata da ido yana karajin gaskiyar zatonsa tana bayyana. Wannan inda ace Baby bata wuce sa'arta ba sai yace itace saboda matukar kamar da sukayi da juna. "No Haris! Kada kayimin haka." Ya fadi a fili kasa kasa,zuciyarsa na tafasa sosai. Suka shige ciki ba tare daya amsa koda gaisuwar da gwaggo keyi mishi ba. Sukaci karo da Mamma ta fito daga kicin. Ta amsa sallamarsu cikin jin dadin rashin ganin Tasleem a falon kamar yanda ta haneta fitowa daga daki har zuwa sadda Kabir zai ba Kzu. "Mahaifiyar Baby kenan." Ya fada a ransa. "A'a yau kuma wa muka samu haka kamar ma ba bakuwar fuska ba a wajena?" Ta fara maganar da duban KB,yayin data karashe tana kallon Baharu. Baharu yayi dariya "Yaya Kabiru ne da,jikan Hajiya kuma aminin surukinki." Magana ta fito! Tasleem da Haris! Wai wanene maci amanata a cikinsu ne? Dakyar suka gaisa da Mamma,baharu ya tambayi Tasleem Mamma kuwa tace bacci takeyi. Kabir murmushi kawai yayi kafin a karshe ya mike yace zai wuce. "Haba dai ko ruwa baka sha ba?" "Bama wannan ba,yace sak'o aka bashi ya bata fa." Cewar Mamma da Baharu. Kabir tuni yayi kofa,ganin haka Baharu ya mara mishi baya. Tuni yakai gate wajen mashin din. Baharu yana zuwa yayi azamar fiddo wayarsa ya bud'o bangaren hotunan tasleem wadanda ma'adanarsu daban ce a wayarsa,dakyar ya lalubo wanda take zaune a falo sanye da doguwar rigar abaya tana dariya ya dauketa domin shi kadai ne mai mutuncin a ciki. Kafadar Baharu ya rike cikin dusashshiyar murya yace "Duba dakyau,itace wannan?" Baharu wanda ya tsorata da yanayin KB yayi saurin duba hoton. "Itace ai amaryar taku." Ya watsawa Baharu mahaukacin kallo kafin ya maida jajayen idanunsa ga gidan. Ashe Tasleem da Haris zasu iya cin amanarsa? Bar maganar Tasleem,yafi mamakin yanda Haris ya munafunceshi ya auri wacce yafi so cikin mata. Ya rantse sai ya dauki mataki koda hakan zaikai ga rabuwarsa da Yasmeen,rabuwar zumuncin iyayensu hakanan da rabuwar wannan amintar tasu da Haris na shekara da shekaru,duk akan 'YAR BARIKI.......!!!!! KARSHEN NA DAYA....!