*UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA ƊAYA Cikin karayar zuciya da ɗacin rai wasu tagwayen hawaye suka fara 'yar tsere a saman dakalin fuskar Baba Isuhu, ya kai kallonsa wurin mai sunan malam da ke wutsul-wutsul a hannun Lami ya ce. "Mai sunan malam ba zan iya rabuwa da kai ba, don Allah Lami kada ki azabtar da ruhina da rashinku." Kuka ya sake ƙwace wa baba Isuhu da ya sauke idanunsa a kan ƙullin kayan Lami da ke ɗaure a ɗankwali. Sai da ya sharce majina da gefen rigarsa sannan ya sake kwantar da murya yana faɗin. "Lami kin san irin so da ƙaunar da nake yi miki? Ko so kike ki mayar da ni marayan ƙarfi da yaji? Matuƙar za ki tafi gidanku sai dai ki tafi da ni Lami, domin ni na fi maye maita indai a kanki ne." Baba Isuhu ya janyo hannun Lami ya haɗa da na mai sunan malam ya rungume a ƙirji sai ya sake ɓarkewa da kuka. "Don Allah ki haƙura da yajin nan da za ki yi Lami. Matuƙar naman ƙauri ne zai datse igiyoyin so da ƙaunar da ke tsakaninmu ko sayar da kaina zan yi, amma na yi miki alƙawari duk inda zan shiga zan yi koma me ye na nemo miki abin ƙaurin nan Lami." Lami ta taɓe ba ki sannan ta ce. "Wallahi Isuhu ba abin da zai hana ni tafiya a daren nan, don in gaya maka na ce wa Goggo Sala ko awa guda ba za mu ƙara a gidan nan ba. Saboda Allah kamar a kaina tsiya ta ƙare, haihuwar fari a ce yau kwana biyu cir babu kajin ƙauri ballantana na saka rai da ɗan akuya ko tinkiya. Kai tir da halinka Isuhu, wallahi da Isa mai tsire na aure na san nama har sai na ci na ture..." Cikin sauri Baba Isuhu ya katse ta. "Me aka yi aka yi Isa ne Lami? Wai ko kin manta Isuhun Lamisuwa mai hadarin naira?" Lami ta sake taɓe baki ta furta. "Ai a banza man kare, tun da a haihuwar ɗanka na fari guda a ce abin ƙauri ya gagara, kenan haka zan zauna har hakikar sunan ita ma ta gagare ni. Wallahi ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa." Jin haka ya sake tsuma Baba Isuhu ya zabure haɗe da ɗaga hannu sama ya ce. "Sai ni isuhullen Lamisuwa mai hadarin nairori, sai ni Isuhun da ya sha gaban zaratan mazaje ya samu Lamisuwa." Lami ta ɗan saki murmushi sannan ya kalle ta ya ce. "Wai ina Lami take?" Da sauri Lami ta amsa. "Ga ni mana." "A yau ba sai gobe ba zan kayar miki da tinkiya." Sai da ya kalli hagu da dama ya yi ƙasa da murya sannan ya matsa saitin kunnenta ya ce. "Kin san Allah yau uwar garke zan girke miki." Da sauri Lami ta washe baki cikin zumuɗi ta furta. "Uwar garke fa..." "Ki yi ƙasa da murya mana haba Lami, ko so kike asirina ya tonu?" Baba Isuhu ya katse ta da sauri. "Ɗan Isuhullena ai sai yanzu na fahimce ka, Allah Ya ba ka sa'a kada hatsabibiyar yarinyar nan ta ganka lokacin da za ka ɗauke mata uwar garken nan." Lami ta yi maganar murya can ƙasa zuciyarta fes. "Ai maso abin ka ya fi ka dabara Lamisuwata, dare zan bi na san yadda zan yi da ita. Ke dai kawai ki zuba wannan ki sha kallo." Baba Isuhu da Lami suka kwashe da dariya. "Lami! Ke Lami ki fito mu wuce kin shanya ni ke 'yar daɗi miji, kin san dai idan ana jego ko kyakkyawan zama a wurin miji ba a yi ballantama wannan mijin na ki..." Lami ta yi saurin katse Goggo Sala, "Goggo zo mu je ciki ai tuni mun riga da mun gyaro ta ni da shi." Baki sake Goggo Sala ta bi ta da kallo sannan ta ce. "Hmmm namiji kenan! Ke yanzu daɗin bakin namiji har zai sa ki zauna..." Lami ta yi saurin yi wa Goggo Sala raɗa a kunne, da sauri Goggo Sala ta washe ba ki ta furta. "Ke 'yar nan da gaske?" Lami ta gyaɗa kai tana murmushe. "Haba ko da na ji wannan ita ce harkar arziƙi, ko ni ƙanwar uwarki ai na samu na lasa wa a bakin salati. Ni fa kin san ni dama na fi kwarkwasa kwaɗayi, duk wurin da ake samun mai maiƙo-maiƙo a nan na fi ƙarfi." Lami ta yi gaba tana tafiya cikin ƙwambo tana jin ita ma ta isa, kuma ta tabbata matuƙar aka wayi gari da an yi mata ƙauri da tinkiya ta san daraja da ƙimarta ta ƙaru a idanun facalolinta. CIKIN DARE A hankali Uwani ta buɗe idonta sakamakon jin fitsarin da ya zame mata kamar farilla cikin talatainin dare, sai da ta gama murtsike idanu sannan ta fara tashin Dada. "Dada! Dada don Allah ki tashi ki raka ni fitsari nake ji." Dada cikin takaici ta saki dogon salati sannan ta ce. "Ni kam wallahi Dijen Iro ta cuce ni da ba ta gashe miki mara tun kina zanin goyo ba, wallahi Uwani ki kiyayi haƙƙin tashina tsakiyar dare da kike yi..." "Dada kamar kukan uwar garke nake ji." Uwani ta katse Dada cikin sauri tana sake kasa kunne, don sama-sama take jin kamar kukan dabbobinta kasancewar suna da ɗan nisa da sashen Dada. Dada ta yi mata shiru saboda takaici. "Dada don Allah ta shi mu je ko wani abu ne yake damun su..." "Ai wallahi ko Umaru ne ya dawo daga Lahira bai isa ya fid da ni waje ba, tun wuri ki kama 'yan matan ƙafafuwanki ki yi gaba." Jin takaicin abin da Dada ta faɗa ya sa Uwani tashi fuuu ta suri buta ta yi waje. Tamkar sabon munafiki haka Baba Isuhu yake tafe cikin sanɗa yana waige har ya ƙarasa sashen da awakin Uwani suke, sai da ya karkace maƙogaro ya maƙe murya kamar yadda Uwani ke yin magana sannan ya ce. "Uwar garkeruruna tayya maza mu je ki ci dusa." Shiru ya ga uwar garke ta yi babu alamin za ta motsa, ganin za ta ɓata masa lokaci ya sa ya ɗago ta ya fara ja a hankali. Sai da ya ƙarasa bakin katanga sannan ya taka turmin da ke jingin, sama-sama ya ɗan fara jiyo motsi don haka ya yi kasake. A ɓangare ɗaya ƙirjinsa na bugawa don kada uwar garke ta yi kuka asirinsa ya tonu. Yana raɓe a gefen katanga ya ga Uwani ta wuce da buta a hannu sannan ya sauke gwauruwar ajiyar zuciya, tirmi ya taka a hankali ya leƙa ya hango Mai gari da ke tsaye yana jiransa. "Haba Isuhu tun ɗazu ɗauko tinkiya ya gagare ka, ko so kake asirinmu ya tonu mutumcina ya bi rariya ya tsiyaye tas a garin nan ina matsayin mai garin garin nan." Baba Isuhu ya yi ƙasa da murya ya ce. "Kai Talle ka san dai fita da uwar garke ta ƙofa ba zai yuwu ba saboda tsaro, yanzu ga ta ka matso zan cicciɓo maka ita." Da sauri Mai gari Talle ya matsa jikin katangar. Baba Isuhu ya koma wurin Uwar garke da ke cin dusa, ya tattaro iya ƙarfinsa ya ɗago ta sai ji kake ɓaaaarrrrrrr wata uwar tusa ta ƙwace masa. Uwani da kawo kanta kenan ta saki murmushi ta ce. "Kai da jin wannan tusar ka san su uwar garke bacci ya yi daɗi." Har za ta gota sai ta leƙa garkensu, sai dai haskarwar da ta yi babu uwar garke babu alamunta. Da sauri ta juyo tana shirin fasa ihu ta hango Baba Isuhu rungume da uwar garke, ita kuma uwar garke jin matsar da Baba Isuhu ya yi mata ya sa ta ware baki ta ce. "Meeeeeeeeehhh." Cikin sauri Baba Isuhu ya miƙa wa Mai gari Talle, Mai gari na karɓa ya fara kici-kicin hawa mashin. Uwani na ganin Baba Isuhu ya miƙa uwar garke ta yi caraf ta kama katanga, sai dai tana gani Mai gari shi da wani da ba ta gane fuskarsa ba suka haye mashin suka fita da gudun gaske. A haukace Uwani ta diro daga kan katangar ta ɗora hannu a kanta cikin tashin hankali ta ce, "Wayyo Allah uwar garkena." Sai kuma ta yi sashen Dada a guje. Ganin haka ya sa Baba Isuhu da sauri ya nufi sashensa. A tsakar ɗaki ya sami Lami don haka tana ganinsa ta ce, "Ya dai Isuhullena an dace kuwa?" Baba Isuhu da ke faman haki ya ce, "Maza ki tafi ɗaki ki kwanta, ni ma lamfo zan yi shegiyar yarinyar nan ta kama mu ni da Talle." Zaro ido waje Lami ta yi ta ce, "Mun shige su Isuhuna ya za ka yi?" "Babu lokaci Lami ke dai ki je ki yi yadda na ce miki." Lami ta yi saurin ficewa shi kuma Baba Isuhu ya faɗa uwar ɗaki ya haye gado sannan ya fara sauke numfashi kamar wanda ya jima yana bacci. "Wayyo uwar garke." Uwani ta furta haɗe da ɓarkewa da matsanancin kuka. Ganin Dada na sakin bacci har da minshari ya sa Uwani ta buga tsalle haɗe da faɗin. "Wayyooo uwar garkena!" Sai a lokacin Dada ta ji ihun Uwani. "Kai ni kam Mamman ya cuce ni da ya haɗa Uwani da kiwo tun tana ƙanƙanuwarta. Yanzu ban da masifa a ce yarinya har cikin bacci tana ambatar tinkiya, wannan bala'in da me ya yi kama..." Dada ba ta ƙarasa magana ba ta ji Uwani ta faɗi a gefen ƙafarta tim! Ta fashe da wani irin matsanancin kuka. A razane ta tashi zaune sannan ta kai hannu ta kunna fitilar ɗakin, hannuwa biyu ta sa ta dafe ƙirji a firgice Dada ta furta. "Uwani ke ce nake gani a gabana ko buɗe mini ido aka yi?" Uwani ta ji tamkar Dada ta watsa mata ruwan zafi, don haka ta fyace majina da gefen zaninta cikin ihu ta ce. "Uwar garkeeeeeena! Baba Isuhu ne uwar garkenaaaa." Dada ta zaro ido waje. "Ke Uwani ko dai gamo kika yi ne? Shi Isuhun ne ya zama uwar garke? An ya lamarinki Uwani babu jifa a ciki?" Dada na gama magana ba ta ji daga bakin Uwani ba ta fashe da kuka tana faɗin. "A'ubikalimatillahi tamma min sharrin ma kalaƙa. Aniya bi aniya wallahi aniyar kowa ta bi shi, Allah Ya kai mu wayewar gari wallahi sai na je gidan Sarkin aska na karɓo miki ƙaiƙayi, ni za a kashe da ƙullutun baƙinciki..." Uwani ta katse Dada daga dogon jawabin da take yi. "Dada wallahi ganin idona Baba Isuhu ya ɗauke mini uwar garke ya miƙa wa Mai gari ta katanga." "Ke yarinyar nan ki ji tsoron Allah, shi Isuhun nawa ne kike jifa da sata? Isuhun da ko yatsa ba za a saka masa a baka ya tauna ba?" Ganin haka ya sa Uwani ta fice daga ɗakin tana faɗin, "Wallahi ko sama da ƙasa za ta haɗe sai ka dawo mini da uwar garkena. Wayyo Allah garkeruruna!" Jikin Dada nan take ya ɗauki karkarwa don haka ta miƙe cikin sauri ta bi bayan Uwani. Kafin wani lokaci wasu daga cikin mutanen gidan suka fara fitowa, kowa ya tambayi Uwani amsa ɗaya take bayarwa 'Uwar garke, Baba Isuhu ya miƙa wa mai gari ta katanga.' Carko-carko suka yi domin ga dukkan alamu sun fara aminta da kalaman Uwani, sakamakon sun duba garken awakinta sun ga babu uwar garke. "Ina shi Isuhun ne?" Baba Idris ya tambaya. Kallon juna suka shiga yi don haka ya bayar da umarnin a je sashen shi a kira shi. Sahabi da Tasi'u ne suka nufi sashen Baba Isuhu, sun jima suna buguwa sannan ya buɗe ƙofa, yamutsa fuska ya hau yi tamkar wanda aka tasa yana bacci ya ce. "Kai waye a tsohon daren nan yake mana bugu haka?" "Baba Isuhu dama Baba ne ya ce a taso ko?" Suka amsa masa. "Ni kuma? A tsohon daren nan? Ko ciwon Yaya ne ya tashi?" Baba Isuhu ya jefa musu tambayoyi kamar bai san abin da yake faruwa ba. Girgiza masa kai suka yi, suka wuce gaba yana biye da su a baya. Yana zuwa ya samu mutane a tsaye carko-carko, tun daga nesa gabansa ke dukan uku-uku amma gudun tonuwar asirinsa sai ya yi hanzarin aro mayafin jarumta ya lulluɓa wa jikinsa. Ya sake aro fuskar mamaki ya ɗora a saman tashi, cikin mamaki ya furta. "Yaya lafiya na ganku haka a tsohon daren nan?" "Uwani ce ta zo mana da wata magana..." Duk abin da ya faru Baba Idris sai da ya zayyane masa sannan ya ɗora da cewar, "Ina Uwar garke take?" Duk da ƙirjinsa bugawa yake amma bai hana shi fututtukewa ba ya ce. "Haba Yaya yanzu duk faɗin gidan nan a rasa wanda za a laƙa wa sata sai ni? Me zan yi da wata uwar garke? Shekarar uwar garke nawa a gidan nan? Amma kawai don yarinyar nan ta shirya ƙaryarta sai a hau kai a zauna, shi kenan tun da ni ne ɓarawon da kuke zargi a faɗa mini nawa ne kuɗinta zan biya." Ganin yadda ran Baba Isuhu ya ɓaci ne ya sanyaya jikin ilahirin mutanen da ke wurin, Dada ta zauna daɓar haɗe da rushewa da matsanancin kuka. "Tsakanina da wannan ɓarawon ni kam sai na kai kukana gaban Ubangiji, ina zaman zamana zai haɗa mini husuma a cikin zuri'ata." Baba Mustafa ya ɗago Dada sannan ya ce, "Yanzu dai duka mu bar maganar nan ni nan zan sayo miki wata ƙatuwar tinkiyar da ta fi uwar garke girma kin ji Uwani." Jin haka ya sa Uwani ta rushe da kuka. "Wallahi ni uwar garke nake so, kuma ko kur'ani aka ba ni zan dafa ganin idona na ga Baba Isuhu da uwar garkena..." Baba Mustafa ya yi saurin katse ta don haka kawai ya ji ya yi na'am da kalaman Uwani, don haka ma ya ce. "To shi kenan ba tinkiya kaɗai zan saya miki ba, kina son ɗan maraƙin sa ko?" Ba don Uwani ta daina jin zafin rashin uwar garke ba ta amsa, sai don son da take wa ɗan maraƙin sa. Saboda haka ta gyaɗa masa kai tana goge hawaye, a gefe ɗaya tana kuma ƙudurtar irin fansar da za ta ɗauka a kan Baba Isuhu don ta yi rantsuwa da Allah jinin Uwar garke ba zai tafi a banza ba. Daga haka gabaɗaya kowa ya watse, Uwani da Dada suka yi sashensu sai dai buta ta sake ɗauka ta fito kamar za ta banɗaki kai tsaye ta wuce sashen Baba Isuhu cikin sanɗa, ta ci sa a bai rufe ƙofa ba don haka tana laɓe daga bakin ƙofar ɗakinsa ta ji Lami na faɗin. "Isuhullena ai ka birge ni da ka ƙaryata shegiya, haka kawai da tuni da tozarta ka a gaban mutane." Baba Isuhu ya saki dariya ya ce. "Ke zan cen da nake miki gobe warhaka mun riga da mun gama ɓarje dabgen kan uwar garke." A gefe ɗaya ta ji muryar Goggo Sala na cewa. "Yanzu dai tun da aikin gama ya gama ai sai ku ja baki ku yi shiru, amma dai Isuhu dole ka badda kama idan za ka shigo da uwar garke don ka san dole a saka maka idanu." Baba Isuhu ya fashe da dariya yana shirin yin magana daga can bayan ƙofa suka ji muryar uwar garke ta ce. "Meeeeeeeeh." A zabure suka kalli juna cikin tashin hankali. "Kukan uwar garke nake ji a tsakar gida Isuhu leƙa ka gani..." Lami ta faɗa da sauri. "Ba ki da hankali Lami, ya za a yi ganin idona Talle ya tafi da uwar garke kuma na ji muryarta ke ki leƙa mana..." Kalaman bakinsa suka katse sakamakon sake jin kukan Uwar garke ta ce, "Meeeeesuhuuuu." Wani abu ne ya tsargawa Baba Isuhu tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar kansa. "Isuhu kamar sunanka na ji a cikin kukan uwar garke." Lami ta faɗa a tsorace. "Meeeeeesuuuhuuuu." Uwani da ke laɓe ta sake maƙale murya ta faɗa da yanayin kukan uwar garke, tana gama faɗa ta dokon ƙauren ɗakin da suke ciki. A zabure Lami, Isuhu da Goggo Sala suka faɗa uwar ɗaki, Goggo Sala da ke ɗaure da ɗaurin ƙirji tun a falo zanin jikinta ya faɗi ba tare da ta sani ba. Goggo Sala da baba Isuhu suka shige bayan ƙofar uwar ɗaki ita kuma Lami ta maƙale a gefen gado, shirun da suka ji ba a ƙara kukan tinkiyar ba ne ya sa suka fara dawowa hayyacinsu. Goggo Sala ta kai idonta jikinta sai a lokacin ta yi ido biyu da tsurar ɗan fatarin (Under wear) da ke ƙugunta, ga ƙirjinta zube a saman kan Baba Isuhu da ke tsugunne a ƙasa. Sai a lokacin ta lura da hannuwan baba Isuhu da ke riƙe da ɗan fatarinta. Cikin matsananciyar kunya ta ce. "Kai Isuhu wanne irin iskanci ne haka saboda Allah za ka nemi shigewa cikin fatarina, ni fa ƙanwar mahaifiyar matarka ce ." Cikin rashin sani Baba Isuhu ya miƙe tsaye sai jin ƙirjin Goggo Sala ya yi a saman fuskarsa, yana ɗagowa suka haɗa ido da ita. Ganin abin kunyar da aka tafka cike da borin kunya ta ce, "Amma dai Isuhu yadda ka kwaso mini ƙirji ina a matsayin sirikarka Allah Ya kwashe maka albarka." 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA BIYU Uwani da ke laɓe tana jin su sai da ta saki murmushi sannan ta wuce ɗakin da Lami da Goggo Sala suke kwana, tana shiga ta samu mai sunan malam yana kwance yana bacci. A hankali ta ɗauko shi sai da ta zo tsakar gida, ta saka shi a cikin ƙatuwar tukunyar da ake dafa wa Lami ruwan wanka amma babu ruwa a ciki. Ta saka hannu ta ɗan jijjiga shi don ya tashi, saboda dama ta jima da sanin Baba Isuhu matsoraci ne na bugawa a jarida, don haka ta gano lagonsa. Baba Isuhu ba ƙaramin ɗacin kalaman Goggo Sala ya ji ba, ya saci kallonta rai a ɓace ya ce. "Allah Ya kwashe mana dai, ni allan-musuru ne na san ke ce a wurin? Wallahi ni da na ji na ɗebo abu a kaina na ɗauka hannuwan Lami ne." Baba Isuhu ya ƙarasa maganar yana fitowa falo. Ya bar Goggo Sala a tsaye cike da takaicin abin ya faɗa. "Tsabar iskanci da wulaƙanci har ƙirjina ya yi lalacewar da za a ɗebo su aka a ɗauka hannuwa ne?" Goggo Sala ta ayyana a ranta. Yana zuwa ya ji mai sunan malam ya tsanyare da kuka. Kusan tare suka kalli juna shi da Lami, sai dai jin shiru babu kukan uwar garken ya sa suka ɗan saki jikinsu. Cikin sanɗa suka fara takawa a hankali har suka fita tsakar gida, suna yunƙurin tafiya ɗaki suka ji kukan mai sunan malam a cikin tukunya ga shi kuma tukunyar a rufe. Lami ce ta yi ƙarfin halin buɗewa nan take ta yi tozali da shi. "Isuhu akwai abin da yake shirin faruwa wallahi." Lami ta faɗa murya na rawa. "Lami ko dai a garin ɗaukar uwar garke ne na tako aljanu? Na shiga uku kada su taɓa mini mai sunan malam." Baba Isuhu ya ƙarasa maganar cikin kuka, Goggo Sala na ƙarasowa suka wassafa mata abin da yake faruwa. "An ya kuwa Isuhu uwar garken ka ɗauka ba aljanu ba kuwa? Gaskiya ruwa ba ya taɓa tsami banza." Cikin Baba Isuhu ya sake ɗurar ruwa, ya waiga a hankali yana kalle-kalle daga can kusurwar bango ya hango kamar mutum a tsaye, Uwani da ke raɓe ganin kar ya gano ta ya sa ta yi wata girgiza haɗe da cewa. "Meeeeesuuuuhuuuu zaaaaan cinyeeeeee idoooonnnnkaaaaa." Jin abin da aka faɗa ya sa Baba Isuhu da su Lami suka faɗa ɗakin da su Lami suke jego. Uwani ta samu ta saɗaɗa sannan ta wuce sashen Dada tana sakin murmushi, ko ba komai ta gano lagwansu da yadda za ta dafa su a ruwan sanyi. Su Baba Isuhu gabaɗayansu babu wanda ya samu sukunin rintsawa, don Baba Isuhu ko sallar asuba bai samu ya fita ba. Sai da gari ya yi haske tarwai sannan suka fito suka yi alwala suka yi sallah, Goggo Sala ta ɗora ruwan wankan mai jego. Ita ma Uwani idonta biyu har aka yi sallar asuba sannan bacci ya yi awon gaba da ita. Ko da gari ya waye babu wata damuwa a tattare da Uwani don ba ƙaramin jin daɗin mafitar da ta samu ta yi ba, ita kanta Dada ta yi mamakin ganin Uwani tana harkokinta. Sai dai a lokacin da ta ƙarasa garken awakinta sun ba ta tausayi musamman da ta ga tagwayen uwar garke sai koke-koke suke alamun suna neman ta, tana zuba musu abinci suka daina kuka sai tagwayen uwar garke da har lokacin ba su daina kuka ba. "Kai Talle asirinmu fa ya kusa tonuwa, kai Allah ne kaɗai ya tarfa wa garinmu nono." Baba Isuhu ya faɗa yana yin ƙasa da murya. "Ai na san za ka gyara komai, kai ma fa shaiɗanin kanka ne. Yanzu dai ya za a yi da kai da ƙafafuwan? Kuma cinyoyin baya ka san na ce maka ni zan ɗauke su." Mai gari Talle ya furta. "Ni yanzu kai da ƙafar 'yar akuya nake so ka samo mini, saboda zan kai wa Dada don na badda idonsu a kaina, cinyoyi dai gaskiya na gaba za ka ɗauka. Kuma sai yamma liƙis za ka aiko min, ka tabbatar an daddatsa komai don kada a fahimci naman babbar tinkiya ne." Mai gari Talle ya gyaɗa kai yana shirin magana ya hango Uwani a ɗan nesa da su tana haɗa tukwanen taɓo, idan ka ga yadda ta mayar da hankali tana wasa sai ka rantse da Allah ba ta san wainar da suke toyawa ba. Ganin ta ya sa Talle Mai gari ya ce. "Abokina ma yi magana anjima kawai, yanzu dai gaskiya sauri nake." Daga haka suka wuce, don shi kansa Baba Isuhu ya lura da Uwani duk da ta yi kamar ba ta san suna yi ba. Uwani na ganin Talle mai gari ya tafi gida ta watsar da kayan ƙasar hannunta, ta sake ɗaure ɗamarar da ta yi da ɗankwali wacce cike take da jelolin raguna da tumakai, da ta shiga kasuwar awaki ta samo. Tana daga jikin katangar ƙofar gidansa ta ga ya shiga soron gidan, da yake turakarsa a soro take don haka a kan idonta ya faɗa ɗakinsa. Tana nan tsaye ta ji ya sake fitowa a tsammaninta fitowa waje zai yi sai ta ji ya shiga cikin gida yana faɗin. "Amarsu ta ango mai daɗin tuwo da miya, wannan ɗan waken da kika shanana mini man ƙuli ai dole na bada tukwici." Da sauri Uwani ta faɗa ɗakin tana shiga ta samu sabuwar langar Zuwaira amaryar mai gari cike da ɗan wake, da sauri ta cakuɗa ta hau ci saboda tsabar ƙeta ta dinga haɗa uku-uku huɗu-huɗu tana ci, cikin ƙanƙanin lokaci ta cinye ɗan waken tas, sannan ta ɗauki ruwa ta sha, ta zaro jelar tumaki biyu ta saka a ciki. Tana shirin miƙewa ta ji alamar tahowar mai gari shi da Zuwaira yana faɗin. "Haba wane mutum ki dinga haɗa kanki da waccen ballagazar. Ke fa komai na ki na daban ne Zuwairatuna." Uwani da ke ɗakin cikin matsananciyar faɗuwar gaba ta shige uwar ɗakinsa, can bayan ƙofa ta ɓuya don ta tabbata matuƙar mai gari ya kamata sai ranta ya yi mummunan ɓaci. Zuwaira cikin kwarkwasa ta zauna tana fari da idanu, hannunta ɗauke da mufici tana yi masa firfita. Mai gari da ƙarfinsa ya ɗauko langa amma jin ta fayau ya sa shi mamaki don ɗan waken da ya gani cike da langa yake, yana ɗaga murfin ya ganshi fayau sai jelar tinkiyoyi a ciki. Wani abu ne ya tsarga masa tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar kansa, cikin faɗuwar gaba ya furta. "Zuwaira kina ganin abin da nake gani kuwa?" Zuwaira da mamaki ya sa ta hangame baki ta ce. "Mai gida me ye wannan kamar jelar tumaki? Ina ɗanwaken da na zuba maka?" Mai gari ya haɗiyi yawu mai ɗaci yana shirin magana daga can uwar ɗakinsa ya ji an ce. "Taaaaalleeeeeeeeeh." Zuwaira ta waiga cike da tsoro ta ce, "Kamar kukan tinkiya kamar kuma cewa aka yi Talleh." Kafin ta gama magana tuni gumi ya gama wanke Mai gari, Zuwaira na shirin sake magana suka ji ƙarar buhu sai kuma Uwani ta sake maƙe murya ta ce. "Ga uwar garke ta dawo ba ta mutu ba, na zo tafiya da talleh a cikin buhun mutuwa." Zuwaira da mai gari nan take suka shiga rige-rigen guduwa, Uwani da ta saka kanta a cikin wani ƙaton buhun gero ta biyo su buguzum-buguzum da gudu tana fisgar malun-malun ɗin mai gari. Mai gari kafin ya shiga cikin gida ya kifa ya kai sau uku, da ya tashi malun-malun sai ta sake harɗe shi. Ladiyo da ke tsakar gida sai ganinsu ta yi a guje. Zuwaira ta shige ɗakinta ta banke ƙofa, yayin da Mai gari ya faɗa ɗakin Ladiyo, yana tafe fitsari da zawo na bin wandonsa. Waige-waige Ladiyo ta fara yi don ita ba ta san gudun da suke yi ba, ganin haka ya sa ta shiga ɗakinta, a can ƙasan gado ta hango Mai gari gumi na yanko masa ta ce. "Mai gida wai me yake faruwa ne?" Mai gari ya sake jan zanin gado don ya rife kansa ya ce. "Ladiyo gamo muka yi a ɗakina, wallahi aljanu ne a ciki." Wani wari ne ya ziyarci hancinta, ta kai kallonta wurin ƙafar wandonsa ta ce. "Mai gida me nake gani kamar zawayi?" "Idan zawayin ne akwai uban da ya yi mini shi? Ba abina ba ne ki bar ni mana Ladiyo." Mai gari ya faɗa yana muzurai. "Don Allah ka taso mu je ka sauya kaya kafin yara su dawo gida." Shiru mai gari ya yi sannan ya ce. "Amma za ki tsaya a ƙofar banɗaki ko?" Ladiyo ta gyaɗa masa kai cike da mamakin wai yau ita Mai gari yake ce wa ta yi masa rakiya banɗaki. Da ƙyar da suɗin goshi Ladiyo ta samu kan Mai gari ya fito, Uwani da ke ɗakin Mai gari har ta fito za ta tafi gida ta ji suna maganar shiga banɗaki. Da sauri ta saki murmushi ta ɗauko buhun ta zagaya ta bayan gidan Mai gari, zuciyarta fes don babu mutane sosai sai waɗansu ƙananan yara da ba su wuce shekara uku ba suna wasa. Kasancewar banɗakin karkara a buɗe yake ta sama ya sa duk abin da Mai gari yake faɗa tana ji, sai da ta tabbata da Mai gari ya tuɓe sannan ta tsugunna ta saitin rariyar ta ce. "Shi kenan ma Talle ya zo masarautarmu da ƙafafuwansa yana wanka, buhun mutuwa zo ka kai Telle inda ya kai shugabarmu wato Uwar garke." Uwani na gama maganar ta watsa masa jelar tumaki biyu ta saman banɗakin, sannan ta wurga ƙaton buhun geron da ta fito da shi. Tana daga nan wurin ta ji Mai gari ya zuba ihu ya fice a guje yana faɗin. "Wayyo Allah! Za su tafi dani, wayyo Ladiyo ki taimaka mini buhun mutuwa ya biyo ni." Garin gudun da Mai gari yake yi ne ta ga takalminsa wari ɗaya ya faɗo ta bayan katanga. Dariya Uwani take yi kamar mahaukaciya sabon kamu, sai da ta yi mai isarta sannan ta ɗauki takalmin mai gari wari ɗayan ta ɗaure shi a cikin ɗankwalin da ke ƙugunta kai tsaye ta wuce gida. Yamma ta yi liƙis a lokacin tana tafe tana waƙoƙinta, da mamaki take bin galleliyar motar da ke ƙofar gidansu. A gaban motar ta tsaya ta isa gaban mudubin motar tana kallon kanta tana yatsine-yatsine, ta mudubin ta hango Salele hannunsa ɗauke da tulu ya ɗebo ruwa. Uwani ta ƙwalla masa kira, nan take jikinsa ya fara rawa, "Yar ƙashin gwiwa don girman Allah ki bari na kai wa Innata ruwan nan." Uwani ta tsuke fuska sannan ta ce. "Don uwarka wani abin na ce maka ne, kawai ka zo na ce ko." Jikinsa a sanyaye ya ƙarasa idonsa na zubar da ƙwallah don ya san yau kwanan tulun Innarsa ya ƙare. Duk abin da yake faruwa Jafar na daga cikin motarsa yana kallonsu, kamar ya yi mata magana sai kuma ya ce bari ya tsaya ya ga iya gudun ruwanta. Don ko ba a ce masa Uwani ba ce, kamaninta da na mahaifinsa ya alamta masa. "Sauke ruwan tulun nan." Ta furta fuska a haɗe. Babu musu Salele ya sauke, Uwani ta fara ɗiban ƙasa tana ƙwaɓawa a saman gilashin motar Jafar, domin baƙin gilas ne kuma ba ta taɓa tsammanin da mutum a ciki ba. A hankali ta fara zuba ruwan tulun tana wanke ƙasar wani wurin ya yi jurwaye wani ya wanku, ta ɗora tulun a saman motar sannan ta ce. "Salele tulun Innarku yau shi zai tuƙa mu zuwa garin Kano, ka san fa sabuwar motata ce da Dada ta sayo mini jiya." Uwani na sakin tulu ya faɗo ƙasa tush! Salele ya wage baki ya saki ihu cikin ɗacin zuciya. A hankali Jafar ya fara zuge gilashin motarsa, Uwani da ke gefe ta yi mutuwar tsaye saboda tsoro don ba ta taɓa tsammanin da mutum a ciki ba. Sai kuma ta maze ta fara harare-harare don kar ya raina ta, ta kalli wurin da Salele yake ihu ta buga masa tsawa. "Za ka yi mini shiru ko sai na mayar da bakinka ƙeya." Tamkar an yi ruwa an ɗauke haka Salele ya yi tsit yana goge ƙwallah. "Uban wa ya ce ki jiƙa mini mota." Uwani ta ji saukar maganar Jafar a kunnenta, ƙirjinta ya buga da ƙarfi saboda tsoro amma don kada ya gano ta sai ta haɗe fuska ta ce. "Ka ga malam bar ganinka da wasu kayan 'yan sanda ka ɗauka za ka tsorata ni, babana ma babban ɗan sanda ne. Wallahi yanzu ihu ɗaya zan yi ya kai ka caji ofis ya sa a kulle ka." Uwani ta ƙarasa maganar tana murguɗa baki, sannan ta yamutsa fuska ganin Jafar ya kafe ta da ido yana kallo ya sa ta ci gaba. "Kai ni fa ban ma yarda da kai ba wallahi, an ya ma kai ba ɗan sandan bogi ba ne? Dubi yadda kake raba idanu kamar shege a rabon gado. Wai ma uban wa ya ce ka jiye mota a ƙofar gidanmu..." Uwani ta haɗiye ragowar kalamanta sakamakon ganin Jafar ya buɗe mota ya fito, ba Uwani ba hatta Salele sai da ya tsorata da yanayin da ya ga Jafar. Uwani a dole don kar ta kunyata kanta ya sa ta cigaba da tsaiwa ta ce. "Ka ga malam tun kashinka bai bushe a hannuna ba ka..." Ta sake haɗiye ragowar kalamanta sakamakon jin Jafar ya damƙi hannunta da ƙarfin gaske. "Yeeeh Uwani ta shiga hannun ɗan sanda." Salele ya faɗa da ƙarfi cikin murna yana tsalle, tuni cikin Uwani ya kaɗa. Salele ya ja baki ya rufe sakamakon ganin bindiga saƙale a gefen aljihun Jafar. Da ƙarfin gaske Jafar ya fisgi hannun Uwani kai tsaye ya wuce cikin gida da ita. Tamkar raƙumi da akala haka Uwani take bin Jafar ƙirjinta na bugawa, zuciyarta na shelar neman agajin gaggawa. Don duk iskancin Uwani tana tsoron bindiga ɗari bisa ɗari. Lokacin da Jafar ya shiga ɗakin Dada babu kowa a ciki, don haka ya wurgar da Uwani gefe fuska a haɗe ya ce. "Maza tashi ki fara tsallen kwaɗo." Uwani jiki na rawa ta fara tsallen kwaɗo sai dai ba ta kai ko ina ba, ta fara hawaye shaɓe-shaɓe. Belt ɗinsa ya ciro yake lafta mata idan ta tsaya, don haka lokaci ɗaya Uwani ta fara fita a hayyacinta. Bayan ta gama tsallen kwaɗo ya saka ta tuƙin babur, da kansa ya gwada mata yadda za ta yi, tana daga tsaye ban da numfarfashin kukan Uwani babu abin da yake ta shi. "Allah mai yau da gobe, wato yau kukan Uwani nake ji a gidan nan? Tabbas gaba da gabanta wai aljani ya taka wuta, Uwani yau wa kika taɓo wanda ya fi ƙarfinki haka..." Kalaman Dada suka maƙale sakamakon ganin Uwani a ƙobare da ƙafafuwa tana tuƙin mashin. Baki a sake Dada ta ce. "Ke Uwani wane sabon iskanci ne kuma haka? 'Ya mace da ke ki hau wani ƙobare ƙafafu kuma kina kuka." Uwani jin abin da Dada ta faɗa ya sa ta faɗi ƙasa ta sake fashe wa da kuka. "Wallahi idan na ƙirga uku ba ki tashi ba sai kin maimaita har da tsallen kwaɗo." Jafar da ke zaune a gadon ƙarfen Dada ya furta fuska a haɗe. A yatsine Dada take kallon wurin ta ce. "Waye haka kuma da baƙaƙen kaya? Na san dai na ba wa Mamman tarbiyya ba zai yi wannan rashin imanin ba, domin ni musulma ce kuma ina sallah a ɗakina amma dubi garsameman ƙato ya shigo mini da waɗannan takalman kalar na arnan Lagas har cikin ɗakina. Wai Jafaru za ka fito ka cire mini takalmi a waje ko sai na kira ubanka mamman ya fitar da kai?" "Dada kada ki sake ɓata mini rai!" Jafar ya furta a takaice. "Ran naka ya fi na ran ƙuda ɓaci, ke Uwani ta shi ki tafi wannan zalinci ba za a yi shi a ɗakina ba. Ni kam wallahi Sa'idu ya gama cutata da ya haɗa mini zuri'a da aikin kaki." Dada ta furta ƙwalla na zuba. Bindigar aljihunsa ya zaro yana juya ta, ganin bindigar ya sa daga Uwani har Dada suka zabura. Hawaye bibbiyu na bin fuskar Dada ta ce, "Yanzu harbe mu za ka yi Jafaru? Ni kam ko ana sauya muku zuciya daga ta musulmai zuwa ta kafirai a wurin tirenin ne?" Jafar ya sake haɗe fuska ya ce. "Ta kanki zan fara ma, Dada sai yau kika san ana sauya mana zuciya?" Ganin yadda ya sha kunu ya sa jikin Dada ya fara karkarwa, Jafar ya fara takowa a hankali kafin ya ƙarasa sai gani ya yi Dada ta zube ƙasa a sume. Murmushin gefen baki ya saki, Uwani na ganin haka ta wage baki ta ƙwalla ihu, a daidai lokacin Malam na madina ya kawo kai yana faɗin. "Wallahi Uwani sai Allah ya yi mana hisabin wannan ihun da kike yi mana babu ji babu gani." Jafar ya hango a tsaye ya mayar da bindigarsa aljihu, yana shirin magana ya hango Dada a yashe a ƙasa. "Na Madina wallahi Jafaru ne ya sa bindiga zai harbe mu shi ne Dada ta faɗi." Uwani ta faɗa fuska da hawaye shaɓe-shaɓe don ba ƙaramin tsorata ta yi ba. Ganin haka ya sa Malam na Madina ya yi wani irin ihun da jaruman indiya suke yi, cikin kukan kura ya yi wata irin sufa ya cukumi wuya Jafar haɗe da maƙale shi yana faɗin. "Wiiiiihuuuuuuhuuuu gafara ga maza nan bisa kanka." 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA UKU Ilahirin ƙarfinsa Malam na Madina ya ware yana cakumar Jafar, idan ya dunƙule hannu sai dai ka ji dum! Ya kai masa dundu a baya. Shi kansa Jafar ya yi mamakin ƙarfin dattijon duk da ba fin ƙarfinsa ya yi ba. Na Madina da ya ga ya ɗauki lokaci bai kai Jafar ƙasa ba, ya zuba wata uwar kabbara tamkar wanda yake tsakiyar yaƙin musulmai da arna yana faɗin. "Allahu Akbar." Da ya yi kabbara sai ya sauke wa Jafar wani dundu a baya. Uwani na ganin haka ta ɗebo ruwa a randa ta fara yayyafawa Dada, babu jimawa Dada ta fara sauke ajiyar zuciya sannan ta buɗe idonta. Jafar tun yana ganin dukan da Na Madina yake yi masa wasa ne har ya ga ya cukwikwiye masa wuya, har wani zullo yake yana kabbara yana kai masa duka tamkar mai jifan shaiɗan. Jafar ya haɗa hannuwan dattijon wuri ɗaya ya murɗe su sannan ya ce. "Wallahi Na Madina ko ka sauko daga kaina ko na bi yatsun hannunka ɗaya bayan ɗaya na tsike su kamar yadda ake tsinkar mangwaro." Jin matsar da Jafar ya yi masa da kuma furucinsa ya sa cikin Na Madina ya karta, yana shirin yin magana ya ji Dada na salati daga kwance. Tamkar ɗan biri sai ga na madina ya yi tsalle ya faɗo ƙasa, Jafar ya gyara wuyar rigarsa ya fice daga ɗakin. Kai tsaye ya wuce ɗakinsa da Dada ta sa aka gyara masa. Malam na Madina ya tsugunna a daidai kan Dada ya ce. "Sannu da farkowa Kulu." Dada ta dube shi luuuu da idanu a shanye sai kawai ta ɗaga ɗan yatsa ɗaya ta ce. "Ashhadu anla'Ila'ha'illahu wa anna Muhammadur Rasulillah." Malam na Madina ya sake cewa. "Mun auna arziƙi Dada wannan yaron ashe harbe ku ya so yi?" Dada ta sake yin luuuu da idanu fuskar na Madina na yi mata gizo ta ce. "Ismi Hauwa kulu wa ana musulima." Jin haka ya sa Na madina ya fashe da kuka, kukan da Dada ta ji ne ya sa ta ɗan wartsake sai a lokacin komai ya fara dawo mata. Zumbur ta tashi zaune ta fara bin su Uwani da kallo. "Uwani kina jin maganata ko kuma da gaske Jafaru ya harbe ni na mutu?" Uwani ta saki dariya ta ce. "Ina jin ki mana Dada ga Na Madina ma a zaune." Dada ta kalli na Madina suna haɗa ido kamar haɗin baki suka fashe da kuka a tare. "Uwani maza ɗauko mini wayata."Dada ta furta cikin kuka. Da sauri Uwani ta ɗauko mata don ta san ba ya wuce ta ce a kira mata baba Mamman. "Maza kira mini Mamman." Uwani ta karɓi wayar ta gama dube-dubenta sannan ta ce, "Lambarsa ce mai hotan zuciya ko?" Da sauri Dada ta gyaɗa kai. Uwani ta kira tana jin an ɗauka ta miƙa wa Dada. "Assalamu Alaikum. Hajiya Dadata yau ke ce da kira da kanki..." "Dakata Mamman! Kiranka na yi ka gaya mini waye shugaban 'yan sanda na duk faɗin duniya?" Dada ta katse Baba Mamman a zafafe. "Shugaban 'yan sanda na duniya? Dada me ya faru kuma?" Ya tambaya a sanyaye. "Me ye ma bai faru ba Mamman? Ka gaya mini shugaban 'yan sanda na duniya da inda zan same shi, domin a yau ba sai gobe ba wallahi zan ce ya tube Jafaru daga wannan aikin kakin. Kai ni dai Sa'idu ya gama cutata, a ce 'ya'ya duka babu mai aiki ƙwaƙƙwara daga Soja, Rosafti sai Ɗan sabda. Wai kamar ni 'yar limamai jikar limamai ace duka 'ya'yana babu limami ko malamin makarantar allo." Sai da Dada ta fyace majina sannan ta cigaba. "Mamman ko ka sa a tube Jafaru ko kuma wallahi sai dai ku nemi wata uwar ba ni ba..." "Don Allah Dada me yake faruwa?" Baba Mamman ya katse ta hankali a tashe. Nan take Dada ta zayyane masa duk abin da ya faru, ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba. Cikin kwantar da murya ya fara lallashinta har ya samu ta daina kukan sannan ta ce. "To yanzu Mamman yadda aiki yake wahala, idan aka tube Jafaru daga aikin nan wacce sana'a zai fara? Tsorona Allah tsorona kada ya fara ɗauke-ɗauke, ni dai na san Jafaru da tsoron Allah ko mage ba zai iya kashewa ba, to ko dai a Lagas ɗin nan ya fara 'yan zuƙe-zuƙe ne da ya zo zai harbe mu?" Murmushi baba Mamman ya yi ya furta. "Dada da ya kashe mana ke ai gara a tube shin kawai, amma dai ba na jin Jafar yana shaye-shaye ki bar ni da shi zan kira shi yanzu a waya wallahi ransa sai ya ɓaci." Dada ta ɗan yi jim sannan ta ce. "Ni fa Mamman ban ce ka kira shi ka yi masa tijara ba, ina zaman zamana Jafaru ya zo ya cika ni da nunkufurcin tsiya. Ni ban san ma lokacin da Saratu ta koya maka masifa ba, yara irinsu Jafaru sai addu'a da lallashi. Kai kanka Mamman ba don tsayuwar da na yi a Harami ba ai da ban san abin da za ka zama ba, Allah dai Ya shirya mana zuri'a." Baba Mamman ya yi murmushi ya amsa mata sannan suka yi sallama. Uwani sam ba haka ta so wayar ta kasance ba, don haka ta miƙe har za ta fita sai kuma ta wuce uwar ɗakin Dada tana sakin murmushi. A can ƙarƙashin gado ta ciro bankinta ta ƙwaƙulo kuɗaɗen da suke ciki, sai da ta ƙirga su kusan dubu ɗaya da ɗari biyar ne. Ta ɗaure su a ɗankwali haka kawai ta fara sakin murmushi, Dada ta bi ta da kallon mamaki baki a sake. Baba Mamman na kashe waya ya kira Jafar ya yi masa faɗa sosai, tare da nuna masa illar tsoratar da Dada da ya yi musamman da shekarunta suka tura. Jafar ya fahimci mahaifinsu sai dai shi tsokanar Dada yake da ya ce harbe ta zai yi. Can ƙasan akwatinsa ya je ya tura bindigar ya ajiye sannan ya shiga banɗaki ya watsa ruwa ya wuce ɗakin Dada. A nan ya shiga tsokanarta suka fara hira har Malam na Madina kamar ba shi ne ya gama kabbara yana naushinsa ba. Uwani na fita can kantin Ɗan bala ta wuce ta sayo alawa irin da raɗin suna leda biyu, sai ta ƙarasa wurin Ali mai dabino shi ma ta sayo gwangwani uku. Sai da ta tsaya a gefen hanya ta kunce kowacce leda ta zuba kofato biyu da ragowar jelar tumaki ɗai-ɗai sannan ta ɗaure. Tana tafe tana sakin murmushi har ta ƙarasa gida, kai tsaye sashen Baba Isuhu ta nufa za ta shiga kenan ta gan shi ya fito da alama masallaci za shi don an kira sallar Magriba. "Sakaryar banza ke ba kya ganin mutane ne?" Baba Isuhu ya furta yana wurga wa Uwani harara. "Ga shi wata mata ta ce na kawo maka." Uwani ta faɗa tana miƙa masa ledar hannunta. Da mamaki ya karɓa ya furta, "Wata mata kuma? Ba kuma Lami aka ce ki kai wa ba?" Uwani ta girgiza kai cikin alamun tsoro ta ce. "Kai ta ce a kawowa kuma ni fa idanun matar ya ban tsoro wallahi, Baba Isuhu dama mutane suna da kofato ne ban taɓa sani ba sai yau?" A firgice Baba Isuhu ya saki ledar alawar ya ce. "Kofato fa? A ina kika ga kofaton?" Uwani na ganin yadda ya firgice sai ta basar ta ce, "Bari dai na wuce wurin Dada..." "Don ubanki za ki tsaya ki mini bayani ko kuwa?" Baba Isuhu ya yi magana jiki na rawa, don bai jima da barin gidan Talle Mai gari ba, da yaje duba shi sakamakon yana kwance sharɓan. Kuma a dubiyar da ya je ne yake shaida masa abin da ya faru da shi a banɗaki da kuma ɗakinsa. "Eh matar ce na ga ƙafarta da kofato, sai ta miƙo mini ledar nan ta ce na ba ka. Kuma ta ce na faɗa maka idan ka wurgar da saƙon nan a kan mai sunan malam za ta fanshe."Da sauri Baba Isuhu ya tsugunna ya fara tattaro dabino da alawar, a nan idanunsa suka ci karo da kofato, tuno abin da Uwani ta faɗa ya sa jikinsa na rawa ya haɗa ledar ya sa a aljihu ya dubi Uwani ya ce. "Ina matar take yanzu." Uwani ta zuba hannu biyu ta yi tagumi ta ce. "Ni fa tana ba ni ledar nan da na waiga sai ban ganta ba, wallahi ina jin ɓacewa ta yi don kamar ƙiftawar ido haka na neme ta na rasa." Wani irin sanyi ƙafafun Baba Isuhu suka yi, Uwani ta yi kamar ba ta gane yanayin da yake ciki ba ta shige cikin gidansa. Baba Isuhu yana nan tsaye har zai fita ko me ya tuna da sauri ya faɗa cikin gida, yana tafe hawaye na zuba don jikinsa ya gama ba shi ta shi ta zo ƙarshe. Uwani na daga ɗakin Lami ta hango shi nan da nan ta ƙunshe dariyarta, yana shiga ɗakin ita kuma Goggo Sala na sirka ruwan wanka don aiki ne ya hana ba ta yi wanka da wuri ba. "Lami ni kam na shiga uku!" Da sauri Lami ta kalle shi, Uwani na jin haka ta muƙe ta fice. Da yake ta lura hankalinsu ba ya kanta kai tsaye ta bi hanyar banɗakin da Goggo Sala ta bi domin yin wanka. Lokacin da Uwani ta je wurin banɗakin Goggo Sala ta riga da ta tuɓe har ta fara wanka, a hankali ta saɗaɗa ta janye kayan da ta cire. Sannan ta fara wani irin gurnani tana kukan tinkiya. Goggo sala ta riga da ta saɓa sabulu a fuska da sauri ta dakata, jin ta daina wankan ya sa Uwani ta yi wani gurnani mai ɗan tsoratarwa sannan ta maƙe murya ta ce. "Gani gare ki Goggo Sala, ki nutsu ki saurari abin da zan faɗa miki domin zai yi miki amfani a matsayinki na jinsin bil'adam." Nan take jikin Goggo Sala ya ɗauki karkarwa kamar mazari, hannu biyu ta sa ta fara kiciniyar goge kumfan fuskarta amma yajin sabulu ya hanata buɗe ido. "Nan wurin da kike wanka masarautarmu ce, kuma kina tsaye ne akan karagar shugabarmu ga hadimanta nan sai zagaye ki suke yi. Wani abin haushi kin saka su kallon tsiraici, don ma Allah Ya taimake ki aljani Manu ɗan kwarto ba ya kusa da tuni ya haike miki." Jin haka ya sa Goggo Sala ta fashe da kuka, Uwani ta gimtse dariyarta ta cigaba da cewa. "Ni ce uwar garke wacce kika dafa namanta, to yanzu haka na dawo domin ni dama ba tinkiya ba ce. Kuma namana da kika dafa a tukunya na ɗauke shi na kai garkena, sannan zan kafa miki wani sharaɗi matuƙar kika saɓa masa zan ɗauke ki zuwa duniyarmu." Goggo Sala baki na rawa ta ce. "To Babata uwar garke faɗi kowanna sharaɗi ne ni mai biyayya ce a gare ki." Uwani ta sa hannu ta toshe dariyarta ta ci gaba da cewa. "Sharaɗin shi ne kullin za ki dinga goya Isuhu sau uku a rana, safe, rana da kuma dare. Idan kika zo goya shi ki dinga yi kina lasar baki, kuma idan kika kuskure koda na lokaci ɗaya ne ba ki yi ba take zan ɗauke ki ko kuma na tsotse romon kanki." "Wallahi zan yi ba dai goyo ba, ko har da Lami aka ce zan haɗa na goya su." Goggo Sala ta faɗa cikin kuka. "Kin taimaki kanki, yanzu kayan da kika cire zan kai shi garkena amma zan bar miki ɗankwali, kuma kada ki kuskura ki fito sai an kira sallar Isha'i domin anfara tattaunawar fadar aljanu da ke. Sannan ɗan autan shugabanmu ya ce da baya da baya za ki tafi ɗaki kina cewa nasara a kanku Isuhu da Lami." Goggo Sala ta amsa, a zuciyar tana da-na-sanin zuwanta zaman daɓaro gidan Lami. Uwani na gama maganar cikin sanɗa ta koma har lokacin baba Isuhu yana ɗakin don ta hango shi ta cikin labule, ta raɓe a gefen ƙofar ɗakin ta karkace murya ta fara kukan tinkiya. Shiru ta ji sun yi sannan ta yi wani gurnani tana yi tana buga ƙafa irin tsalle-tsallen da awaki suke yi. "Shi kenan Lami ta zo ina jin tafiya za ta yi da ni." Baba isuhu ya faɗa cikin kuka. "Ba zan tafi da kai yanzu ba. Ni uwar garke ni ce na aiko maka da saƙo ɗazu. Ku buɗe kunnenku da kyau, uwar garke ba mutum ba ce. Na zo na kafa muku sharuɗɗana idan kuka bi su zan yafe muku zunubin da kuka aikata mini, idan ba haka ba kuma a gabanku zan yi farfesun mai sunan malam na saka ku cinye shi kuma ku shanye romonsa." "Wallahi ko mene ne kika ce mu yi za mu yi miki biyayya." Lami ta faɗa a tsorace. "Kai Isuhu da farko taimakonka za mu fara yi kafin ka ji sharaɗinmu. Ƙanwar mahifiyar matarka babbar matsafiya ce a ɓoye, kuma dama da biyu ta zo zaman daɓaro gidanka. Idan kuma ka yi yunƙurin korarta za ta halakaka da iyalinka gaba ɗaya. Daga gobe ne wa'adin aikin da take yi a kanka zai fara, don haka yanzu ma za ku ga ta fito tana tafiya da baya-baya tana ambatar sunanku don haka kada wanda ya tanka mata. Kuma gobe za ta zo da sassafe ta ce maka za ta goya ka. Duk rintsi kada ka bari ta taɓa maka jikinka." A zabure Baba Isuhu ya ce. "Goyo fa? Ni Isuhu za a goya da giramana ban da iskanci?" Uwani ta katse shi. "Idan muna magana ba a tankawa. Sannan Sharaɗin da za mu kafa maka ya zama wajibi ka ɗauki rigunan mama na Lami guda uku ka kai wa mahaifiyarka Dada ka ce ta saka su..." "Dadar ce za ta saka bireziya..." Baba Isuhu ya furta cikin suɓutar baki. Uwani ta buga masa tsawa cikin gurnani ta ce. "Idan ka saɓa mana wallahi sai mun hallaka ka da kisa mafi muni." Nan take Baba Isuhu ya ce. "Duk abin da kika ce na bi Inna uwar garke." "Na dawo gare ki Lami. Ke kuma akwai dafin da Goggo Sala ta saka miki a ruwan wanka wanda wa'adinsa gobe zai cika, ko ba kya ganin irin maganin da take zuba miki a ruwan wanka kullin?" Da sauri Lami ta gyaɗa kai. "Idan kika sake shayar da ai sunan Malam daga gobe ke da shi mutuwa za ku yi, domin dodonta zai zuƙe jininku tas." Da yake Lami ta san Goggo Sala da shegen bin malamai nan take ta aminta da kalaman Uwani. "Sharaɗin da zan kafa miki ya zama dole daga gobe ki dinga ɗaukan mai suna Malam kina kai wa Jafar shi yana shayar da shi a sashen Dada." Cikin haɗin baki Lami da Baba Isuhu suka ce. "Jafaru kuma? Shi zai shayar da mai sunan Malam?" "To kada ku kai shi dama ɗan autan Goɗiya kwaɗayin romon jariri yake ji sai na dafe masa shi." Uwani ta faɗa cikin wata irin murya, don ita kanta dagewa take da tuni dariya ta kwace mata. "Wallahi za mu kai shi, Allah Ya kai mu gobe." Gabaɗaya suka amsa. "Kuma ya zama wajibi a gare ka, kai Isuhu ka saka ƙarfi ka danne Jafar domin a shayar da mai sunan malam idan ba haka ba komai zai iya biyo baya. Kuma sharaɗin da zan kafa muku na ƙarshe ko da wasa kuka faɗi abin da ya faru tsakanina da ku, sai na sa wuƙar aljanin mahauta ya yaɗe fatar jikinku sannan na ɗauke ku zuwa duniyarmu a azabtar da ku kamar yadda kuka azabtar da ni." Uwani na daga tsaye ta fara jiyo shasshekar kukan Baba Isuhu. Sai da ta lallaɓa ta ɗauke tukunyar naman da aka yi farfe su ta ajiye a soro sannan ta ce. "Tukunyar namana da kuka dafa ku same ta a wurin garkena, kada wanda ya fito har sai an kira sallar isha'i domin tuni an zauna zaman fadar aljanu da ku. Kuma idan kuka bari namana da kuka dafa ya kwana a garkena cikin dare zan gayyato tawagar jinsinmu su ɗauke mini ku." Uwani na gama maganar ta fara kukan tumaki tana wani irin dire-dire sannan ta ɗauki tukuyar ta tafi a hankali, kai tsaye ta wuce garken awakinta. Da yake duhu ya yi awakin Uwani duka sun kwanta, a hankali ta isa turken uwar garke ta ajiye tukunyar. Ta janyo igiyar uwar garke ta saƙale a jikin ƙafar tukunyar, zuciyarta fes ta wuce sashen Dada don ta yi sallar magriba tana tafe tana dariya kamar sabuwar kamu. Har alla-alla take gari ya waye ta ga irin diramar da za a tashi da ita. A lokacin da ta shiga ɗakin Dada Jafar na zaune ta kofin shayi a gefensa , ga laptop a gabansa yana dannawa, dawowarsa daga masallaci kenan. Uwani na ƙare masa kallo ta tuntsire da wata mahaukaciyar dariya, domin yanayin zaman da ta ga ya yi ne har ta hango yadda Baba Isuhu zai danne shi a shayar da mai sunan malam. Ɗagowa ya yi ya kalle ta sai kuma ya ci gaba da danna laptop ɗinsa, Uwani ta sake kallonsa ta ga yadda yake jin magani sai kawai ta tsugunna a wurin tana sheƙa uwar dariya. "Uban me kike yi wa dariya?" Jafar ya furta a daƙile. Tamkar wacce ya sake ingizawa, sai Uwani ta sake fashewa da dariya har da hawaye da ta tuna duk irin haɗe fuskar da yake yi wai shi za a danne a shayar da mai sunan malam. "Ba tambayarki nake yi ba?" Jafar ya buga mata tsawa. "Dama wani wasa ne muka fara bugawa ni da ƙawata Lantana shi ne na shirya mata yadda zan cinye ta gobe." Uwani ta yi maganar tana ɗan murguɗa baki. "Ba na son shashanci idan wannan iskanci za ki yi ki fice mini ba na son hayaniya." Uwani ba ta kula shi ba ta gimtse dariyarta ta shige uwar ɗakin Dada. Ku kawo wa Jafar ɗauki zai shayar da mai sunan malam🤭🏃🏼‍♀️😂 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA HUƊU Tun da Uwani ta fito daga gidan baba Isuhu daga shi har Lami babu wanda ya kuma motsin kirki, baba Isuhu ya sharɓe hawaye ya dubi Lami cikin kallon tsana da jin haushi ya ce. "Tsakanina da ke Allah Ya isa Lami, kin cuce ni kin cuci rayuwata. Ni ban san ƙaddarar da ta sa na auro ki ba, duk wannan ƙaton bakin na ki ko ina ya je da ban gan shi ba sai yanzu?" Lami ta wurga masa harara ta ce. "Mun dai cuci juna malam ka gyara maganarka. Ni kaina ban azal da kuma rabo me zan yi da kai? Ka san dai duk a samarina kai ne faƙiri matsiyaci." "Wallahi aurena da ke bai ƙare ni da komai ba sai masifa, ina zaman zamana kin jefa ni a jafa'i muguwa mai ƙashin tsiya..." "Dakata malam, kada ka raina mini hankali. An gaya maka ban san dama can kana 'yan sace-sacenka ba? Ko ka manta kajin Yaya Haladu da muka taɓa soyewa?" Shiru baba Isuhu ya yi yana nazari, shi kam ya ci alwashin daga uwar garke har abada ba zai ƙara taɓa kayan wani ba. Dama tun da yake 'yan ɗauke-daukensa ba a taɓa kama shi ba, don haka zai ajiye sata salin-alin ba tare da ta tona masa asiri ba. Suna nan zaune suka ji an rafka kiran sallar Isha'i, babu jimawa suka ji takun Goggo Sala tana tafe da baya-baya, taku ɗaya-biyu idan ta yi sai ta ci karo da kwanuka sannan ta furta. "Nasara dai a kanku Isuhu da Lami." Da hannu Lami ta yafito baba Isuhu ta cikin labule take nuna masa ita, cikin gasgata maganar da Uwani ta gaya musu suka saki baki suna kallonta, a ɓangare ɗaya kuma tsoron Goggo Sala ya kama su. Tana shiga ɗakin da suke kwana da Lami ta banko ƙofa, can ƙuryar bango ta zauna sai kawai ta rushe da wani irin kuka mai cin zuciya. "Kaico kwaɗayina bai amfane ni da komai ba, Allah ka fitar da ni daga wannan gidan annobar. Wallahi nan gaba idan duniya Lami za ta haifa har abada ni da gidanta." Ganin ta shige ɗaki ya sa baba Isuhu ya fita a hankali domin cika umarnin uwar garke, kai tsaye garken Uwani ya nufa yana haskawa kuwa ya yi ido biyu da tukunyar farfesun naman. Nan take ƙirjinsa ya buga, jikinsa ya fara karkarwa sai da ya yi ta maza ya ɗauko tukunyar ya nufi sashensa. WASHEGARI Baba Isuhu tun da ya yi sallar asuba ya gagara runtsawa saboda fargabar goyon da Goggo Sala za ta yi masa, yana zaune a gefen gado ya kallo Lami da ke kwance ita da mai sunan malam. Motsi ya ji a tsakar gida yana leƙawa ya hangi Goggo Sala tana kaiwa da kawowa, abin duniya ya dame ta saboda gari ya fara haske amma har kawo lokacin babu Isuhu babu motsinsa. Cikin sanɗa ta nufo ɗakin da suke ciki baba Isuhu ya leƙo ta windo ya ce. "Munafukar Allah ta'ala ina ankare da ke, wato fakona kike za ki hallaka ni ko?" Goggo Sala ta washe baki tana basarwa ta ce. "Isuhu barka da safiya." Baba Isuhu da ya tuna gargaɗin da aka masa, aka ce kar ya yi mata kora da hali shi ma sai ya yaƙe baki ya amsa. Amma a zuciyarsa ji yake tamkar ya fashe da kuka. Mai sunan malam ne ya motsa Lami ta yi fitgigit ta tashi zaune. "Maza tashi mu je ki kai shi wurin Jafaru." Ba musu Lami ta tashi ta saka hijabinta, baba Isuhu ya manta Goggo Sala da ke waje tana fakonsa ya sa hannu ya buɗe sakata suka fito. Har zai yi gaba ya tuna bai ɗebo rigunan maman Lami da aka ce ya kai wa Dada ba, dama tun a daren ya sa Lami ta ɗebo masa guda uku daga cikin na ta. Komawa ya yi ya ɗebo ya zuba a aljihu sannan ya fito. Yana fitowa Goggo Sala ta yi wata uwar sufa za ta cafko baba Isuhu, a firgice ya zuba a guje yana faɗin. "Wayyo Lami ki zo za ta cafke ni, wallahi tsaf za ta sa a tsotse romon kaina." Goggo Sala na ganin rana ta fara fitowa ga shi ba ta cika umarnin uwar garke ba, ya sa ta rufa wa baba Isuhu baya yana gudu tana bin sa. Da yake ya gama tsorata da ita har gani yake kamanin Goggo Sala kamar har rikiɗe masa suke yi, Goggo Sala irin dogayen matan nan ne, shi kuma baba Isuhu ba shi da tsayi kuma ba shi da jiki. Don haka Goggo Sala ta kusa kama shi amma Allah ya taimake shi ya fice daga gidan, Lami ta rufa masa baya da sauri ya tura ƙofar ya datse ta. Wata gwaruwar ajiyar zuciya ya sauke yana ayyana shi kenan da tuni an bayar da jininsa. Ɓangaren Dada a buɗe yake don haka ba su sha wata wahala ba suka nufi ɗakin da Jafar yake ciki, Lami ce ta fara ƙwanƙwasawa sun ɗan jima sannan Jafar ya buɗe da alama bacci yake yi. Daga shi sai singlet da gajeren wando ya buɗe ƙofar yana murza idanu. Da mamaki yake bin su Baba Isuhu da kallo ya furta. "Ina kwana baba." Baba Isuhu ya washe baki. "Jafaru an tashi lafiya?" Jafar ya amsa sai baba Isuhu ya ce. "Wurinka muka zo Jafaru amma ko za mu ƙarasa ɗakin Dada?" Zuciyar Jafar fes ya ce. "Ok to bari na saka kaya ga ni nan zuwa." Lami da baba Isuhu suka wuce ɗakin Dada a lokacin tana zaune tana jan carbi. Tana ganinsu ta shafa addu'ar, sai da ta cire hijabin ta ajiye carbin ta ce. "Isuhu lafiya na gan ku da farar safiyar nan?" Cikin haɗin baki suka gaishe ta. Baba Isuhu ya ciro rigunan maman hannunsa ya miƙa wa Dada ya ce. "Dada ga wannan a saka." Dada ta karɓa tana yamutsa fuska. "Kai kuwa Isuhu kamar wanda ya kwana da Uwani a rai, tun da farar safiya ka kawo mata wata rigar mama. Wannan dai rigunan ai na manyan mata ne, ina Uwani ina wannan lalacewar." Baba Isuhu ya ɗan sosa kai ya ce, "Ai dama ba na Uwani ba ne, ke na kawowa Dada..." Tun bai ƙarasa magana ba Dada ta katse shi, "Ni fa Isuhu? Ni kuwa me zan yi da rigar mama tsofai-tsafai? Amma dai ka ci mutumcina Isuhu, wai ko dai ka fara 'yan zuƙe-zuƙe ban sani ba?" Idanun baba Isuhu suka ciko da ƙwalla sai da ya share hawaye ya ce. "Don girman Allah Dada ki ɗiba ki shiga ɗaki ki saka." Baki sake Dada take kallonsa, ta rafka salati haɗe da faɗin, "Maza kwashe mini lalatattun kayan nan kafin ranka ya ɓaci. Ni Kulu uban me zan saka a ciki? An ya Isuhu shaɗanu ba su dafa maka kai a cikin bacci ba?" Uwani da ke uwar ɗaki ta sunne kai ƙasa tana dariya. "Haba Dada da farar safiya ki cika wa mutane kunne da ihu." Jafar ya faɗa yana sako kansa cikin ɗakin. Uwani da ke ɓoye a ɗaki ta yi ƙasa da murya ta ce, "Kai ma naka ihun yana tafe." "Ba dole ka ji ihuna ba Jafaru yanzu kamar ni tsofai-tsofai." Sai kuka ya ci ƙarfin Dada sai da ta share hawaye sannan ta watsa wa Jafar rigunan a fuska ta ci gaba. "Wai Isuhu ya rasa me zai kawo mini sai baraziya wai na saka. Yanzu saboda Allah Jafaru ko uwarka Saratu me za ta yi da baraziyya ballantana kuma ni?" Tun Dada ba ta gama magana ba Jafar ya watsar da rigunan sakamakon wani tsami da bashi-bashi da ya ji ya doko hancinsa. "Haba Dada me kike yi haka ne?" Jafar ya faɗa a ƙazance. Kafin Dada ta yi magana mai sunan Malam ya sake tsanyarewa da kuka, Lami ta dubi Jafar ta miƙa masa shi. Kamar Jafar zai yi magana sai kuma ya basar ya miƙa hannu ya karɓe shi, yana bin su da kallon mamaki. "Don Allah Jafaru ka taimaki yaron nan ka ba shi mama ya sha ko ya yi shiru." Lami ta faɗa a ɗan kunyace. Jafar ya kalli Lami cikin sauri ya ce. "Wane Jafarun?" Jafar ya tambaya a hargitse. "Kai mana Jafaru, don Allah ka yi ka ba shi kada ya shiɗe don tun ɗazu yake kuka." Baba Isuhu ya furta. Ran Jafar ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, ya haɗe fuska ya dubi baba Isuhu. "Baba wannan wacce irin magana ce babu tsari, yanzu idan na faɗa maka magana a ce na yi rashin kunya. Idan har ni zan iya shayar da shi me ya hana kai ba ka shayar da shi ba?" Dada ta saki baki da hanci tana kallon baba Isuhu a tsorace, don ita a yanzu ya fara ba ta tsoro shi da Lami. A hankali ya ajiye mai sunan malam a gefe sannan ya miƙe, yana shirin tafiya Lami ta ce. "Isuhu sai fa mun danne shi..." Tun Lami ba ta ƙarasa magana ba baba Isuhu ya sa ƙafa ya shatalo ƙafar Jafar sai ga Jafar a ƙasa. Dada na ganin haka ta fara tafiya da rarrafe don ta tabbata yau su Isuhu babu lafiya, shi ya sa ta nemi guduwa kafin ita ma su dawo kanta su danne ta su saka mata rigar mama. Jafar ya yi mamakin yadda ya gagara ƙwace kansa a hannun baba Isuhu, don haka jin baba Isuhu ya fara ɗaga masa riga sama ya fara kiciniyar kare kansa, garin yunƙurin danne rigarsa sai ga Jafar yana sakin tusa. Uwani kuwa me za ta yi ba dariya ba har hawaye saboda mugunta. Ganin haka ba zai kai Jafar ba ya sa ya fara ihu. "Wayyo Dada ki kawo mini ɗauki. Wayyo Allah! Mutanen gidan nan ku kawo min ɗauki su Lami za su haike mini." Uwani na daga ɗaki ban da dariya babu abin da take sheƙawa, saboda tsabar dariya har kwanciya ta yi ƙasa. Suna cikin haka sai jin muryar Goggo Sala suka yi a bakin ƙofa ta fara lashe baki tana faɗin, "Allah na gode maka da har yanzu lokaci bai ƙure mini ba." A zabure baba Isuhu ya ɗaga Jafar, take jikinsa ya fara karkarwa ta fara tunkaro shi yana ja da baya. "Wayyo Allah Dada ki zo Goggo Sala za ta sa a cinye ni." A madadin Jafar ya gudu tun da ya samu ya tsira sai ya bi baba Isuhu da kallo, saboda ba ƙaramin mamaki ya ba shi ba. Dada da ke cikin ɗaki ta kai wa Uwani duka tana ce wa. "Dariyar me kike yi Uwani mu da ya kamata mu fara yunƙurin ƙwatar kanmu." Kafin Uwani ta yi magana suka ji baba Isuhu ya zuba ihu. "Wayyo ta shanye mini ƙafafu, Jafaru, Dada ku zo ku kawo mini ɗauki." Goggo Sala ba ta bi ta kan baba Isuhu ba ta shatalo ƙafafuwansa za ta sunkuta shi a baya sai ga baba Mustafa da baba Idris sun shigo. "Subhanallahi kai Isuhu lafiya kuwa?" Suka ƙarasa maganar suna ƙarasawa wurin Goggo Sala, baba Isuhu da yake ya gama tsorata sai ji suka yi sharaf ya faɗo jikinsu da alama ya suma. Suka kama shi suka kwantar a ƙasa sai kawai Goggo Sala ta fashe da kuka. "Yanzu shi kenan rayuwata ta zo ƙarshe." Da mamaki suke bin ta da kallo, Baba Mustafa ya dubi Jafar da ya yi laƙwas a gefe ya ce. "Kai Jafar wane sakarci ne haka ake yi kai kuma kana zaune?" Jafar ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Baba ni ma ta kaina nake da tuni sun haike mini, dube ni wai fa ni zan shayar da mai sunan Malam." "Gara da Allah Ya kawo ku Idirisa, wallahi Isuhu shi da matarsa sun haukace. Ashe ba su kaɗai ba har da Salamatu ita ma, an ya ba gamo suka yi a cikin gidan ba. Ban da haka wai ni Isuhu zai kawowa rigar mama ya ce na saka, sannan su dubi garjejen ƙato kamar Jafaru su ce ya shayar da me sunan malam." Baba Mustafa ya yi farat ya ce. "Shi Jafarun ne zai shayar da jariri?" Dada ta wara hannuwa ta furta. "Ta ya ni ji dai Muɗɗafa, ka ga dai a kan idona aka haifi Jafaru. Kai ƙarshe ma dai ni na yi jinyar shayin da aka yi masa ballantana na ce ko Jafaru ya koma mata-maza, Jafaru ko ka sauya daga baya zuwa mata-maza ne ban sani ba." A ƙufule Jafar ya ce, "Wallahi Dada kar ki ƙara ce mini mata-maza." Kukan da mai sunan malam yake tsanyarawa ne ya sa baba Idris ya yi wa Lami magana, sai da ta share ƙwallar idonta ta ce. "An ce daga jiya kada na ƙara shayar da shi." A daidai lokacin baba Isuhu ya farfaɗo sakamakon ruwan da aka yayyafa masa. "Waye ya hana ki shayar da shi?" Shiru gabaɗaya suka yi, baba Isuhu ya dubi Lami ita kuma ta kalli Goggo Sala sai kawai suka fashe da kuka lokaci ɗaya. Shiru ɗakin ya yi kowa yana bin su da kallon mamaki, ban da Uwani da ke sakin murmushi a fakaice. Sai da suka yi me isar su sannan aka samu da ƙyar Goggo Sala ta ce. "Ni kam na san wannan jawabin da zan yi ƙila shi ne na ƙarshe a rayuwata don na san kashe ni za su yi." Baba Isuhu ya yi tsammanin bayanin 'yan ƙungiyar asirin da take ciki za ta faɗa, don haka ya zuba mata ido sai ya ji ta ce. "Dama dai uwar garke ba..." Kamar haɗin ba ki Lami da Isuhu suka ta fi da gudu suka toshe mata baki, da mamaki mutanen ɗakin suka bi su da kallo. "Ƙarya take yi makira haɗa ni da 'yan uwana za ta yi." Baba Isuhu ya faɗa yana haki kamar wanda ya ci gasar tseren gudu. "Ba ma son shashancin banza da wofi Isuhu, sakar mata baki kada ranka ya yi mummunan ɓaci." Baba Mustafa ya faɗa a fusace. Babu yadda suka iya haka suka koma suka zauna jiki a sanyaye, baba Isuhu ya sunkuyar da kai ƙasa gabansa na faɗuwa. Goggo sala ta fara wassafo jawabi tiryen-tiryen tana hawaye. Tana gama jawabi gabaɗaya ɗakin suka ɗauki salati. "Kaico rayuwa ni Kulu me na haɗa da sata da Isuhu zai janyo mini mugun hali cikin zuri'ata." Dada ta furta tana zubar da ƙwallah. Malam na Madina da ke gefe ya ce. "An ya Isuhu yanzu rayuwar da ka ɗauko mana kenan? Wallahi ka yi gaggawar yin istigifari kuma ka nemi masu kaya ka mayar musu da abin su. Idan ba haka ba muna cikin Firdausi kana Hawiya, atoh faɗar Allah ce ba ya yafe haƙƙin wani a kan wani." Shiru ɗakin ya yi kunyar duniya ta mamaye baba Isuhu shi da su Lami. Baba Idiris da baba Mustafa suka rufe shi da faɗa sosai, don haka ya nuna nadamarsa a fili. Sannan baba Mustafa ya juyo wurin Dada. "Dada ki gafarce ni a game da abin da zan faɗa amma tun farko ke ce kika ɓata Isuhu, saboda Isuhu yana ɗan autanki kika ɗauki son duniya kika ɗora masa. Hatta makaranta da Baba Sa'idu ya saka shi daina zuwa ya yi kuma kika goya masa baya, duk cikinmu shi kaɗai ne bai samu karatun arabi da boko mai zurfi ba. Ga shi nan sana'o'in ma wacce ce ba a nuna masa ba amma kullin a tsalle-tsalle yake ba shi da aiki sai kame-kame, tun wuri ka yi wa kanka faɗa domin kullin girma kake ƙara yi." Dada ta sharce ƙwallar da ke fuskarta ta ce. "Yanzu dama Muɗɗafa ka na da tarin nasihohin nan tutuni ba ka yi mini ba? Ni dai wannan maganar a rufe ta a nan kada Sa'idu ya ji don wallahi sai ya kusa cinye ni ɗanya." Gabaɗaya suka amsa mata. "Dama wannan abin kunyar ai ba za mu bari ya fita ba Dada, yanzu dai a tambayi Uwani tun da haƙƙinta ne ta yafe masa?" Uwani da ke gefe ta saki murmushin ƙeta ta yi saurin cewa, "Ni dai Baba na riga da na yafe musu baba Isuhu ai tamkar mahaifina na ɗauke shi." Da sauri Jafar ya dube ta don haka kawai ya ji bai yarda da kalaman Uwani ba. "Allah Ya yi miki albarka Uwani, dama ɗa ba sai wanda ka haifa ba kaico rayuwa Allah Ya gafarta wa Yaya Umaru." Baba Isuhu ya faɗa yana sharce ƙwallah. Uwani ta saki murmushin ƙeta a ranta ta ce, "Za ka ga ɗa ba sai ka haifa ba." Baba Idris ya yi musu nasiha sannan ya ce shi da kansa a ranar zai kira su Aramma na gangare su yi saukar Alƙur'ani a gidan gabaɗaya. "Baba ni fa gani nake wannan abin da aka yi musu kawai tsoratarwa ne wani ke yi musu, idan aljanun gasken ne ai da tuni sun ɗauki mataki. Kada a yi wasa da hankulan mutane a dai duba lamarin." Jafar ya yi maganar yana zuba wa Uwani kallon tuhuma, don yadda ya ga tana sakin murmushi ya ji sam bai yarda da ita ba. "Koma dai mene ne ai babu abin da ya fi ƙarfin Ubangiji Jafaru. Allah Ya yi mana maganin wannan masifa." Baba Mustafa ya faɗa, gabaɗaya suka amsa da Amin. Uwani na haɗa ido da Jafar ta sakar masa harara, haɗe da murguɗa masa baki. 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA BIYAR Kasancewar sunan gidan baba Isuhu ya zo a lokacin hutun zangon karatu ya sa ilahirin zuri'ar gidan sun hallara, musamman da ya kasance baba Mamman ya dawo gida ne gabaɗaya domin lokacin ritayarsa ta kusa. Kuma a wannan kwanakin ne yake shirin tarewa a katafaren gidan da ya gina a nan cikin Unguwar rijiyar zaki da ke jihar Kano. Hajiya Saratu da iyalanta sai shan ƙamshi suke yi suna kallon mutane ɗaiɗai, don ko maganar arziƙi ba ta cika haɗa ta da sauran facalolinta ba. Sanin halinta na raini da wulaƙanci ya sa suma sauran mutanen gidan suke kama mutumcinsu ba tare da sun shiga sabgarta ba. Asalin Tarihinsu Malam Haruna mai shanu shi ne ainihin cikakken sun marigayi malam mahaifin su baba Isuhu. Asalinsa mutumin garin Rigana ne da ke cikin ƙauyen lambar ƙunci, ɗaya daga cikin ƙananan ƙauyukan da ke jihar Kanon Dabon Najeriya. Sunan mai shanu ya samo asali ne tun a wurin mahaifinsa kasancewarsa fitaccen bafulani a wannan ƙauyen, duk girman garin Rigana babu mai albarkar shanu da dabbobinsa. Yana da matar aure ɗaya da 'ya'ya biyu sakancewar duka maza, Malam Haruna shi ne babba sai ƙaninsa mai bin sa Sa'idu wanda bayan su mahaifinsu bai sake haihuwa ba. Bayan mahaifiyar su malam mahaifinsu ya auri mata biyu sai dai ko ɓatan wata babu wacce ta taɓa yi. Mahaifiyarsu ta rasu tun suna samari yayin da mahaifinsu ya rasu bayan da kowannen su ya yi aure a lokacin Malam haihuwarsa biyu. Baffajo tun da ƙuruciyarsa yakan ɗebi shanu da awakinsa su tafi garuruwa kiwo bayan wani lokaci sai ya dawo gida, hakan yake yi har zuwa lokacin da su Malam suka zama samari suma yake nuna musu hanyar kiwon shanu. Sai dai tun suna yara ya fahimci sam ba su da ra'ayin kiwace-kiwacen shanun da yake yi, bayan da mahaifinsu ya rasu sai suka ɗora daga inda ya tsaya sai dai su ba kamar Baffajo ba. Don tun bayan da ya rasu bai fi sau uku zuwa huɗu suka fita da shanu zuwa wasu garuruwan ba. A wannan lokacin ne kuma watarana bayan malam ya fita da shanun su da suka gada a wurin mahaifinsu, ya yi nisa sosai da garinsu sai ya faɗa tarkon wasu 'yan fashin daji. Kasancewar kuma sarkin yawa ya fi sarƙin ƙarfi sai suka yi masa ƙwacen shanu da yawa, kaɗan ya rage ba su hallaka shi ba ya dawo gida da tsirarun shanun da ko goma ba su kai ba. Wannan yanayin da suka shiga wasu sun dasa zargin har da saka hannun mutanen garinsu, yayin da wasu kuma suka ce jarabta ce kawai daga wurin Ubangiji. Dalili kenan da ya sa bayan da malam ya warke suka haɗa kai shi da ɗan uwansa suka bar garin gabaɗaya tare da sayar da shanunsu, suka dawo wani ɗan ƙauye a nan garin Kura suka kafa kasuwancin su. Kuma cikin hukuncin Ubangiji sai Allah ya saka musu albarka. Hauwa kulu Ibrahim mai allo shi ne cikakken ainihin sunan Dada asalinta mutuniyar garin Bauchi ce, baƙar bafulatana ce tana da kyau daidai gwargwado. Mahifinta Malamijo ɗan gidan malamai ne domin a rigarsu gidan su Dada ba ɓoyayyan gida ba ne. Mahaifinta yana da mata biyu da 'ya'ya bakwai. Musa shi ne ainihin sunan malam na Madina, kuma shi ne babban yayansu Dada uwarsu ɗaya ubansu ɗaya. Ya auri matarsa bayan zamansu mai tsawo Allah Ya yi mata rasuwa, sai dai bayan ita ya yi aure-aure da dama bai taɓa samun haihuwa ba. Dada ita take bin shi sai kuma Fatsime take bin Dada sai dai akwai tazara sosai tsakanin Dada da Fatsime. Fatsime ta rasu a wurin haihuwa, ta rasu ta bar 'yarta Abuwa dalilin da ya sa Dada ita da na Madina kaɗai suka rage waɗanda suke uwa ɗaya uba ɗaya. A lokacin da mahaifiyar su Dada ta haifi Fatsime har ta cire rai da sake samun haihuwa. Hasiya, Safare, Sule da Gali sune sauran 'yan uwan Dada da suke Uba ɗaya. Malam ya haɗu da Dada ne a lokacin da suka tafi kiwo garin Bauchi tun mahaifinsu na raye, don haka ba a ɗauki lokaci ba aka tsayar da maganar aure bayan wani lokaci aka ɗaura musu aure. Da yake Dada nesa da garinsu za a kai ta sai mahaifinta ya haɗa ta da ƙanwarta Fatsime, a kan bayan wani lokaci idan Dada ta saba sai Fatsime ta dawo. Sai dai ko da Malamijo ya buƙaci Fatsime ta dawo malam da kanshi ya je har garin Bauchi ya roƙi arziƙin a bar musu Fatsime a wurin su. Ganin yadda malam ke kula da Dada da kuma girman da yake ba shi sai ya kawar da kai ya haƙura ya bar masa ita. Dada da malam sun haifi 'ya'ya tara bakwai maza sai biyu mata. Baba Yunusa (Soja ne), baba Mustafa (Road safety ne), baba Idris (Malamin makarantar secondry ne), baba Mamman (Ɗan sanda), baba Rufa'i (Likita), Atika, Halimatu, marigayi Umaru wato mahaifin Uwani sai kuma Baba Isuhu (Sayar da itace yake yi). Baba Sa'idu (Ƙanin malam) Yana da mata ɗaya da 'ya'ya biyar. Biyu maza sai uku mata. Ya auri matarsa ne tun a garin Rigana, kuma tin bayan komawarsu Kura da suka fara kasuwanci shi da ɗan'uwansa, sai ya fara tafiye-tafiye zuwa garuruwa. Sannu a hankali sai nemansa ya fi ƙarfi a garin Zaria, don haka ya ɗauki iyalinsa suka koma can da zama. Cikin ikon Allah kowannensu ya ci gaba da zama da iyalinsa. Da yake Dada kwanika ta dinga yi gabaɗaya 'ya'yanta tazarar su babu yawa, kuma a lokacin da take da cikin Baba Isuhu ne Allah ya yi wa malam rasuwa. Kafin rasuwarsa ne ya biya mata Makka, zuwan farko umara ta je ta yi sai zuwa na biyu da suka je tare suka yi aikin Hajji. Malam Sa'idu ya kaɗu da rashin ɗan uwansa domin ko mutuwar mahaifinsu ba ta bige shi haka ba, daga nan kuma ya riƙe dukiyar ɗan uwansa da amana yana juya musu. Kuma ya ci gaba da tallafa wa Dada ita da yaranta, ya tsaya musu kai da fata suka samu ilimin addini da na zamani kuma har Allah ya ci da su suka samu aikin yi. Sai dai ba da aikin Gwamnati kaɗai suka dogara ba domin suna harkar kasuwancin kayan robobi da harkar kayan abinci. Baba Mamman yana da matar aure ɗaya Hajiya Saratu da yara biyar. Jafar shi ne babba, Ibrahim, Shukra, Jidda, sai Mufida wacce suke kira da Auta. Hajiya Saratu 'yar aminiyar mahaifin baba Mamman ce, ba ta da son mutane ko kaɗan. Mace ce mai faɗin rai da taƙama uwa-uba tana da son kanta, ga ta da tsananin kishi sannan akwai ta son hulɗa da matan masu kuɗi. Wannan halin na ta ya sa ko kaɗan ba ta jituwa da Dada, kuma kusan halayenta ne su Shukra suka kwasa gabaɗaya. Jafar da Ibrahim ne ba su da irin halinta sai Auta don haka har sun fi su Shukra sabo da mutanen cikin gida. Gidan marigayi malam Haruna mai shanu gidan gandu ne da ya haɗa kakanni, iyaye, jikoki da kuma 'ya'yan jikoki. Baba Mamman da Baba Yunusa ne kaɗai ba sa zaune a cikin gidan, kasancewar yanayin aikinsu da sauye-sauyen garuruwan da ake yi musu a wurin aiki. Amma kowannensu yana da ɓangarensa a cikin gidan, idan suka zo hutu suna sauka da iyalansu a ciki. Marigayi Umaru Haruna Mai shanu shi ne mahaifin Uwani, ya rasu tun mahaifiyar Uwani na da cikinta wata bakwai sakamakon hatsarin mota. Maryama Shu'aibu shi ne ainihin sunan mahaifiyar Uwani, dalilin mutuwar mahaifin Uwani ya sa Dada da su Baba Mamman suka ci gaba da kula da ita. Bayan wata tara Allah Ya sauke ta lafiya ta haifi jaririyarta, ta ci burin idan namiji ne ta mayar da sunan mijinta Umaru. Amma da ta haifi mace su Dada suka tambaye ta sunan da take son a raɗa wa jaririyar, da kanta ta ce a saka sunan Dada saboda irin karamcin da suka nuna mata, sai ake kiranta da suna Uwani. Bayan da aka yaye Uwani ne mahaifin Maryama ya nemi da ta dawo gabansa da zama, domin zawarawa suna ta zuwa kai masa gaisuwa da nuna ƙoƙon bararsu a kan aurenta. Ranar da za ta tafi ne Dada ta nemi da ta bar mata Uwani saboda soyayyar da take yi wa mahaifinta, idan tana ganinta za ta dinga jin daɗi. Bayan komawar mahaifiyar Uwani gidansu ko shekara ba ta rufa ba aka ɗaura mata aure da wani mutum, a lokacin yana da aure da mata ɗaya da yara huɗu. Maryama ta aure shi ne ba don tana son shi ba, sai don kawai ta yi wa mahaifinta biyayya amma har lokacin zuciyarta na ga mahaifin Uwani. Garin da take aure yana nesa da garin su Uwani sosai, kuma ta haifi yara biyu da malam Salihu mace da namiji, sai dai ko kaɗan ita da kishiyarta ba sa jin daɗin zama da shi sakamakon mugun halinsa. Uwani ta taso a hannun Dada cikin kulawa da nuna tsantsar soyayya, tun bayan tafiyar mahaifiyarta baba Mamman ya so a ba shi riƙon Uwani amma fir Dada ta hana shi, lokacin da Hajiya Saratu ta ji ba ƙaramin daɗi ta ji ba. Shekarun Uwani goma sha huɗu a duniya kuma irin fitinannun yaran nan da suke fita zakka ko a cikin unguwa. Rashin ji, rashin tsoro, kafiya, naci, tsokana rashin yafiya sune halayen da suka mamaye Uwani har mutanen garin suka saka mata suna 'Uwani 'Yar Ƙashin Gwiwa' saboda hatsabibanci da rashin jin ta. Duk cikin gidan mai shanu Dada ce kaɗai ba ta ganin laifin Uwani, don haka ma duk wurin da ta shiga sai dai su bi ta da harara. Jafar ma'aikacin ɗan sanda ne mai ɗauke da muƙamin ASP, shekarunsa talatin da biyu cif a duniya. Ya yi karatunsa tun daga primary har zuwa matakin degree a jami'ar Bayero University. Miskili ne bai cika surutu ba, sai dai wani lokacin bauɗaɗɗan hali gare shi. Yana da kirki ga wanda suka fahimci juna sai dai wani lokacin yana da saurin fushi. Ba ya son raini ko kaɗan kuma yana da kykkyawar mu'amala da abokan aikinsa. Lokacin da ya fara aiki jihar Kaduna aka tura shi bayan wani lokaci ne ya samu sauyin aiki zuwa garin Katsina daga baya aka mayar da shi garin Lagos, ya kwana biyu a Lagos don bai cika zuwa hutu sosai ba. Ko da ya zo ma a gurguje yake kawo wa Dada ziyara shi ya sa Uwani ba ta wani san shi farin sani ba. Tana yawan jin labarin irin kulawar da Jafar ɗin ya dinga ba ta a lokacin da take yarinya, sai dai a wannan karon sam ba ta ga kalar mutumci a tattare da shi ba. Wannan hutun da Jafar ya samu kusan wata guda zai yi kafin ya koma, kuma ya ji labarin zuwan mahaifansa hutu da tariyarsu don haka shi ma ya yada zango a nan sashen Dada. Mu Koma Labari Tamkar sabuwar munafuka ko ɓarawon da yake sanɗa a daidai gaɓar da yake ɗaukar abin da ba na shi ba, haka Uwani ta shiga cikin ɗakin saɗaf-saɗaf tana tafe tana waige. Sai da ta kai ga ƙuryar ɗakin sannan ta sauke gwauruwar ajiyar zuciya. "Uban 'yan iyayi ashe ba ya cikin ɗakin, da tuni yana nan a naɗe a kan katifa kamar mai karyayyan ƙugu." Ta furta cikun salon kwaikwayon muryarsa. Motsin da ta ji a bayanta ne ya sa ta yi mutuwar tsaye, zuciyarta ta fara harbawa tamkar za ta bijirewa zama a ƙirjinta, cikinta ya shiga juyawa yayin da zazzafan gumi ya shiga keto mata. Caran zakaran da ta ji a bayanta ne ya sa ta sake sauke ajiyar zuciya, ta saki murmushi a fili sannan ta furta. "Lawan wallahi ka cika binbinin tsiya, yanzu ɗakin Ofisa ma sai ka biyo ni. Idan kuwa ya kama mu wallahi sai ya kusa murɗe maka wuya." Tamkar zakaran ya san da shi take ya ci gaba da takawa yana tafe yana sakin kashi a tsaftataccan ɗakin da ya sha gyara ta ko ina sai zuba ƙamshi yake.   Kafin Uwani ta ƙarasa kan katifar ɗakin tuni zakaranta da take kira da Lawan ya yi mata jagora zuwa kan luntsumemiyar katifar da ta sha gyara, a ɗame take da zanin gado kamar gadon sabuwar amaryar da za a kai ɗakin miji. "Lawan ina ka baro Fanteka, uwar 'ya'ya na san tana cen tana yawo ita da 'ya'yan iya." Uwani ta yi maganar kamar da mutum ɗan'uwanta take yi. A saƙale ta hango uniform ɗinsa na kayan 'yan sanda masu bulun riga da baƙin wando. Da sauri ta janyo ta hau kwaɓe kayanta kafin wani lokaci tuni ta saka a jikinta, sai da ta gama soshe kanta da ya cukurkuɗe sannan ta kafa baƙar hularsa a kanta. Cikin ƙwambo ta fara taku ɗaiɗai sannan ta cake a wuri ɗaya. "Ba na son hayani matsa daga kaina, ƙazama mai kwarkwata." Ta yi maganar cikin kwaikwayar maganar Jafar, tana faɗin irin maganganun da yake faɗa mata.  Ta jima a tsaye tana surutanta sannan ta ƙarasa gaban mudubin da ke can gefenta, kamar a mafarki haka ta hange shi tsaye ƙyam kamar wanda ya haɗiyi falwaya. Fuska a haɗe kwatankwacin ta fusataccan bujumin sa. Nan take yawun bakinta ya ƙafe, ƙafafuwanta suka ɗauki rawa ƙirjinta ya shiga harbawa. Sai dai dakiya da ƙarfin zuciyar Uwani ya sa ta basar kamar ba ta gan shi ba. "Iya iya iya." Ta ji 'ya'yan kazarta na faɗa yayin da zakaran da ya gama kasaye ɗakin ya fara cara, da sauri kazar ta tunkaro ɗakin da niyyar shiga a fusace Jafar ya sa ƙafa ya yi ball da ita. Wata azababbiyar ƙara Uwani ta ƙwalla kamar da ita Jafar ya yi ball, ta fara tafiya wandon uniform ɗin yana zamo mata. "Innalillahi kashe mini fantake za ka yi..." Uwani ta yi maganar tana shirin fita daga ɗakin, yayin da Lawan (Zakaranta) ya firgice yana tsalle-tsalle a ɗakin, yana jefo masa kwalaben turare. "Gidan uban wa za ki?"Jafar ya wurga mata tambaya rai a ɓace. "Ina da gidan da ya wuce ɗakin Dada..." Jafar ya katse maganarta ta hanyar bige bakinta da ƙarfi. "Wallahi na ba ki nan da minti goma ki gyara mini ɗakin nan, sannan ki yi gaggawar cire mini uniform tun ranki bai ɓaci ba. Kuma idan kin gama zan gauraya da ke." "Sai ka fita na canza kaya." Sororo ya yi yana kallon Uwani don bai san lokacin da ta raina shi ba. Yana shirin sauke yatsunsa biyar a fuskarta wandon uniform ɗin ya zamo mata, gajeren wandon da ke jikinta ya bayyana. Fari ne amma dauɗa da jirwaye sun sa ya dafe saboda ƙazanta. A ƙazance ya kawar da kai gefe haɗe da tofar da yawu. "Ka san dai kallon tsiraici haramun ne, ka fita na sauya kaya. Kuma ni dai ba 'yar iska ba ce..." "Idan ba ki rufe mini baki ba wallahi sai na haɗa miki jini da majina a wurin nan. Sakarya fuska kamar ta aljanu, daga yau ko wani ne ya aiko ki ɗakin nan ba za ki ƙara marmarin shigowa ba." Tun da Jafar ya fara magana Uwani take kallonsa sheƙeƙe tun daga sama har zuwa yatsu biyar na ƙafarsa. Ba ta yi aune ba ta ji ya zuba mata rankwashin da ya sa ta gagara gane muhallin da take tsaye. Cikin sauri ta fisge hular kanta, ta zame dogon wandon uniform ɗinsa da ke jikinta. Jafar na nan tsaye ya ji tuuush! Lawan ya jefo sabuwar kwalbar turarensa, a firgice yake miƙa wuya yana cara haɗe da ci gaba da taka kayan da ke saman mudubin. A zuciye Jafara ya jefa masa takalmin kanbas ɗinsa. Firgitar da Lawan ya yi har cikin ran Uwani don haka cikin ɓacin rai ta ce, "Allah dai ba ya zalinci yana kallon baƙaƙen azzuluman duniya masu baƙaƙen kaya." A fusace Jafar ya yo kanta rai a ɓace, ganin haka ya sa Uwani ta zuba a guje kai tsaye ta wuce sashen Dada Jafar ya rufa mata baya. A daidai lokacin da Jafar ya nufi sashen Dada shi kuma malam na Madina ya kawo kai, cikin rashin sani Jafar ya bangaje shi kaɗan ya rage gemunsa ya taɓa ƙasa. "Jafaru! Kai Jafaru kana ji ka angije ni kamar ka angije dabba? Wallahi duk laifin Kulu ne ni take nunawa 'ya'ya da jikoki sun fi ɗan uwa." Ya ci gaba da tafiya har bakin ƙofar Dada yana kiran sunanta. "Kulu! Kulu kina ina ne..." Cikin sauri Malam na Madina ya datse ragowar kalaman bakinsa jin furucin da Jafar ke faɗa.   "Wallahi tun wuri ki wuce mu je ɗakina don har kan katifa..." Uwani ta yi farat ta katse shi. "Amma dai ai ka bari na saka kayana yaya Jafaru, wallahi na fita a haka ka san dai mutanen gidan nan kowa sai ya san abin da yake faruwa." Jafar ya yi ƙwafa yana shirin ba ta amsa daga can waje ya ji muryar Malam na Madina yana sallallami. "Yanzu Jafaru dama munafurcin da kuke aikatawa kenan? Shi ya sa saboda sauri har ka angije ni ko waige na ba ka yi ba. Ba da ni ba, wallahi ba zan zauna ana aikata alfasha ina kallo ba, lokaci ɗaya Ubangiji ya halakar da mu." Sai da Jafar ya fito daga ɗakin Dada ya samu Malam na Madina da ke bin shi da ƙazantaccan kallo. Ficewa ya yi daga sashen Dada ya faɗa ɗakinsa, akwatin kayansa ya janyo ƙiiiiii yana kokawar fito da ita Dada ta sako kai ciki. Jin motsin ya yi yawa ya sa ta fara mita. "Waɗannan dabbobi na Uwani yadda kasan tare aka shayar da su saboda duk hatsabibancinsu iri ɗaya ne..." Ganin Malam na Madina ya janyo akwatinsa ƙiiii ya sa Dada sakin baki, "Wai Muda ne a wurin nan ko Usumanu?" Ta wurga masa tambaya tana ɗan ƙanƙance ido. Sai da Malam na Madina ya fito sannan ya ce. "Ki yafe ni Kulu don kar na tafi da haƙƙin wani a kaina." Baki sake Dada ta ce, "Yaya wani abin aka yi maka ne?" Malam na Madina ya share ƙwallar idonsa, ta waiga wurin da Jafar yake tsaye a bakin ƙofa ya jefa masa mugun kallo sannan ya furta. "Ubangiji aka yi wa laifi, ni dai tsakanina da mutanen gidan idan na ce an yi mini wani abu na ɗauki haƙƙinsu. Amma ni kam ba zan zauna ina ji ina gani a dinga saɓon Allah ba, gara na mutu salin-alin da a tashi idanuwa su bada shaidar baɗala ranar Lahira." Malam na Madina na gama magana ya fara jan akwatinsa ƙiiiii, da sauri Dada ta sha gabansa don tuni hankalinta ya tashi idonta ya fara ciko da ƙwalla. A duniya idan akwai abin ta tsana shi ne a ɓata ran Malam na Madina. Jafar ya kafe Malam da kallo yana jin kamar ya ƙarasa ya shaƙe shi ko ya rufe shi da duka. "A duniyar nan dai Yaya ka san mu biyu kaɗai muka rage, kuma kai ne uwata kai ne ubana kai nake gani na huce rashin su marigayi, (Iyayensu) don Allah ka faɗa mini abin da yake faruwa."Dada ta yi maganar tana share ƙwalla. "Waye wancan a tsaye?" Na Madina ya nuna Jafar a daidai lokacin Uwani ta leƙo don jin abin da yake faruwa daga ita sai gajeren wandon jikinta, ta tuɓe riga ta rufa hijabinta a saman ƙirjinta. Dada ta kai kallonta wurin ta ce, "Jafaru ne sai Uwani da ta fito." "Amma a rigar kwasam na san ba za ki manta Iron Alto ba?" A firgice Dada ta kalle shi, ba ita ba hatta Jafar ya san labarin Iron Alto a bakin Dada. Dada na shirin magana Malam na Madina ya katse ta. "To Ta'adar Iron Alto na ji waɗannan yaran suna aikatawa..." Tun bai rufe baki ba Dada ta saki butar hannunta wacce ta ɗauro alwala da ita jiki na rawa. Yau dai bari mu tsagaita dariyar na ga jiya har da masu shiɗewa 😂 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA SHIDA Dada ta zuba musu ido ganin yanayin da Uwani take ciki ya sa ta aminta da kalaman ɗan'uwanta, ta san dai ba zai taɓa yi musu ƙarya ba. Runtse idonsa Jafar ya yi yana fesar da iska mai zafi, ya buɗe idanunsa da suka rine jawur kamar gauta ya sauke su a kan malam Na Madina. A fusace ya ƙarasa gabansa ya cukwikwiyo babbar rigarsa ya riƙe shi wuri ɗaya rai a ɓace ya furta. "Wallahi ba don ina duba tsufanka ba, da yau sai na bambamce maka tsakanin zuma da maɗaci." Jafar ya sake shi sannan ya wuce ɗakinsa, saboda tsoro tuni malam Na Madina ya yi mutuwar tsaye. Dada ta bi bayan Jafar da kallon tsoro baki a sake. "Yaya an ya Jafaruna ne ba aljanu ne a kansa ba..." Kuka ya katse maganar da Dada take yi. "Sharrin ƙwaya ce Kulu, na sha faɗa miki wannan aikin ɗamarar ba zai haifar da samun ɗa mai ido a cikin zuri'armu ba. Yanzu wa gari ya waya? A ce Jafaru bai san Kano garin Musulunci ba ne? Ya ɗauka rayuwar da yake yi a Legas ita zai yi a gidan nan. Kin ga dai abin da ya faru a gabanki. Da fa dukana zai yi, kaico rashin haihuwa ne ya ja mini haka." Na Madina ya fashe da kuka, Uwani da ke gefe ko a jikinta ta shige ɗaki ta ci gaba da sauya kaya. Don ita hakan da ya faru ma daɗi ta ji, ko ba komai ta san Jafar da zuciya ba lallai ya sake shiga sashen Dada ba sai bayan kwana biyu, ballantana ya hora ta a kan laifin da ta yi masa. Tana gama sauya kaya ta fice a nan harabar gidan ta ga Lawan da matarsa Fanteka, 'ya'yan ta ɗibo ta yi hanyar keji da su uwar ta rufa musu baya. Sai da ta dawo ta ga Lawan yana tsince-tsince a wurin akuyoyinta. "Kai dai Lawan ka cika ɗan kishiya riƙon mai haƙuri, wallahi da kiwon ka aka ba ni da ka ja mini zagi a ce na bar ka da yunwa." Uwani ta yi maganar tana ƙoƙarin kama shi, Lawan ya yi tsalle zai dira a kan katangar gidan Baba Isuhu da ƙyar ta kama shi tana sakin murmushi. Kai tsaye sashen Dada ta wuce tana shiga ta ci karo da Jafar ya fito ɗauke da jaka a kafaɗa.   "Marar gaskiya ko a ruwa gumi yake. Yaya ka ga yaron nan saboda ya san tsiyar da ya shuka fita zai yi ya bar mu, ni dai wallahi Sa'idu ya cuce ni duk wannan abin da yake faruwa Sa'idu ne sila." Jafar bai bi ta kan su Dada ba ya fice daga gidan har yana hankaɗe Uwani. "Kulu Allah Ya ba mu alheri, wallahi Jafaru ba zai yi mana turun jeka ka mutu ba. Ya shuka bishiyar tsiya mu da ba mu ji ba, ba mu gani ba mu girbe masa." Malam na Madina ya sake jan jaka ganin haka ya sa Dada ta ce. "Ka jira ni yanzu zan kira Inusa dole ya tara mini 'yan'uwansa a gidan." Dada ta yi maganar tana faɗawa ɗaki domin ɗauko wayarta. "Inusa a yanzu ba sai gobe ba ka tara mini 'yan'uwanka, wallahi idan ba haka ba zan bar muku gidanku na shiga duniya. Kuma ku yi gaggawar kiran Jafaru ku ce ya dawo don zaman nasu ne, shi da Uwani ne suka ƙulla tsiyar da bakina ba zai iya furtawa ba." Daga haka Dada ba ta sake cewa uffan ba ta kashe wayarta, da kashe wayar babu jimawa Baba Yunusa ya sake kiranta, Dada na ɗauka ta ce. "Yunusa wai wa muke yi wa Sallah da azumi?" Daga can ɓangaren Baba Yunusa ya ce. "Allah." Dada ta sake haɗe fuska kamar yana ganinta ta ce. "Da ma saboda na fita haƙƙinka a matsayinka na babba shi ya sa na kira na sanar da kai, wallahi idan ba ka haɗo mini kan 'yan uwanka ba sai dai ku nemi wata uwar ba ni ba." Dada za ta katse da sauri Baba Yunusa ya ce. "Shi kenan Dada ga mu nan zuwa yanzu In shaa Allah." Ta amsa masa sannan ta katse wayar, sai da ta lallami Na Madina sannan ya mayar sa akwatinsa. Falon tsit ya yi da ka kalli fuskokinsu ka san kowanne yana cikin damuwa, Baba Yunusa ne ya yi  ƙarfin halin cewa. "Dada gaba ɗaya ga mu mun hallara." Jafar tun da ya sunkuyar da kai ƙasa zuciyarsa ke tururi, Uwani na raɓe a gefe sai raba ido take kamar ƙosan sadaka. Ganin haka ya sa jikinsu ya sake yin sanyi, don sun tabbata banza ba ta kai zomo kasuwa.   Sai da Na Madina ya kalli Jafar da Uwani sai ya sake fashewa da kuka, ganin haka ya sake raunata zuciyar Dada ta ja gefen mayafi ta fara sharce hawaye sannan ta fara magana. "Gabaɗayanku na tabbata idan za ku yi mini shaidar Allah da Annabi, za ku yarda da abin da zan faɗa." Suka amsa mata cikin haɗin baki. Dada ta ci gaba da ce wa. "Wallahi ƙanin mahaifinku Sa'idu ya cuce ni cutar ta har abada, amma ya je ba ni ya yi wa ba zumuncin Allah ya yi wa kuma ranar gobe ƙiyama sai igiyar zumunci ta zarge shi. Ni dai ba zan shiga tsakaninsa da Ubangiji ba amma sai mun tsaya a gaban Ubangiji ni da shi." Sororo gaba ɗaya suka yi hankali a tashe suna kallonta. Baba Yunusa ya ce. "Dada me yake faruwa haka ne Baba Sa'idu fa? Baba Sa'idu da ya zame mana bango madafa kuma majingina, mutumin da ya maye gurbin mahaifinmu..." "Inusa wa ya samar maka aikin Sojan nan? Kuma wa ya samarwa ɗan'uwanka Mamman aikin Ɗansanda, shi kuma wancan Rosofti?" Dada ta Katse shi. "Duka Baba Sa'idu ne ya samar mana Dada wani abu ne ya faru?" Ya tambaye ta a sanyaye. "Aikin ɗamarar ba shi ya kai Jafaru Lagas ba?" Duka suka amsa mata, jin furucin Dada ya sa Jafar ya ɗago a fusace. Dada ta cigaba da faɗin. "Silar haka ai ga shi muna shirin samun Iron Alto na biyu a cikin gidan nan." Jin kalaman Dada ya sa gaba ɗaya suka ɗauki salati hankali a tashe. Baba Isuhu ya wurga wa Jafaru wani mugun kallo cike da ƙyama, yana riƙe da haɓa hannunsa ɗaya kuma na riƙe da mai sunan Malam. Sai da ɗakin ya lafa da hayaniyar da ake yi sannan Na Madina ya ce, "Wallahi ba tun yau ba shi ya sa magana ta a kullin yaran nan a aurar da su, amma da yake nasara ya hure muku kunne sai ku ce yara sai sun yi karatu. Yanzu dubi garsamemen ƙato kamar Jafaru a ce bai yi auren fari ba, ni wallahi ina kamarsa da Allah Ya ba ni haihuwa da na yi 'ya'ya uku. To yanzu me ya fi wannan haushi? Wa ya sani ma a Lagas ɗin ko 'ya'yan ƙedarai ne suka suke buɗe masa idanu, yake wartar ɗaya bayan ɗaya yana sakayewa a gefe. Ga shi nan yanzu ai ya gagara haƙuri ya ja Uwani ɗakin Kulu suna watsa wa sunnar Ma'aiki ƙasa a ido." Kamar haɗin baki gabaɗaya mutanen ɗakin suka furta. "Innalillahi Wa'inna ilahirraji'un."   Duk budurin da ake yi ko a jikin Uwani ita babbar damuwarta ba ta wuce ta samu ta tsira daga horon Jafar ba, don ta san yadda ransa ya ɓaci idan ta shiga hannunsa sai Allah. Ran Jafar ya kai matuƙar ƙololuwar ɓaci don haka a zuciye ya buga tsaki haɗe da miƙewa zai fice daga ɗakin. "Wallahi matuƙar Jafaru ya fita daga ɗakin nan Mamman sai ka bi ɗanka, tun da ni da ɗan'uwana ba mu isa da shi ba." Dada ta yi furucin rai a ɓace. "Koma ka zauna Jafar." Mahaifinsa ya furta murya a dashe saboda ɓacin rai.   "Daddy wai ba ka ji me waɗannan mutanen suke faɗa ba ne? Wannan wanne irin abu ne. A ce a rasa ƙazafin da za a yi mini sai na zina, kuma na rasa da wa zan yi sai Uwani yarinyar da ƙazanta ta samu gurbin zama a ilahirin jikinta..." Na Madina ya katse Jafar sakamakon rarrafowar da ya yi, ya dafa ƙafarsa. Kwanciya na Madina ya yi a gabansa sannan ya fashe da kuka. "Don Allah kada wanda ya hana Jafaru ya rufe ni da duka, dama ɗazu ka so dukana to ka saka bindiga ka tashi kaina a kan waɗannan magangun da kake faɗa mana ni da 'yar uwata." Na madina ya furta ƙwallah na zuba, idan ka ga yadda yake rusar kuka sai ka rantse da Allah wani abin aka yi masa. "Ba na son sakarci ka koma ka zauna Jafar." Mahaifin Jafar ya buga masa tsawa. Sai da ya haɗiyi yawu mai ɗaci sannan ya koma ya zauna yana wurga wa su Na Madina harara, ya sunkuyar da kai ƙasa cikin ɓacin rai. Baba Inusa da kansa ya ƙarasa ya tashi Na madina ya koma mazauninsa sannan shi ma ya koma ya zauna.    Baba Rufa'i ya gyara zama, sannan ya fara magana. "Dada duk mun ji abin abin da yake faruwa amma don Allah ku gafarce ni a maganar da zan faɗa." "Kayya Rufa'i muke wa Ubangiji laifi ma ya yafe mana, ballantana ɗan'adam abin banza." Cewar Dada. "A iya sanin tarbiyyar da yaran nan suke da ita ba mu taɓa tsammanin haka za ta taɓa faruwa ba, sai dai kuma ɗa ne ka haife shi ba ka haifi halinsa ba." Dada ta jinjina kai jin kalaman Baba Rufa'i yana shirin ci gaba da magana ta katse shi. "Ai albasa ce ba ta yi halin ruwa ba Rufa'i, wai a rasa wurin da za a yaye wa sunna labulen albarka sai a ɗakina. Kaico ni Kulu." Sai da Dada ta yi shiru sannan ya ɗora. "Kai Jafar ina maka kallon mai hankali ya aika yi haka ta faru?" Kai tsaye Jafar ya nuna su Dada murya a shaƙe ya ce. "Baba a tambaye su ni kaina sama ta ka na ji abin da suke faɗa." "Ba ni da ɗan uwana ka ƙaryata ba, uwarka Saro da ubanka Mamman su ka ƙaryata ka ji Jafaru." Dada ta furta tana wurgawa Jafar taƙuwa. "Ka shiga taitayinka Jafar? Idan na kuma jin magana mara daɗi daga bakinka sai ranka ya yi mummunan ɓaci, ke Uwani shin yau wannan abin ya taɓa shiga tsakaninki da Jafar ne?" Baba Rufa'i ya jefa mata tambaya. Zuciyar Uwani ɗaya ta share ƙwalla ta ce, "Wallahi ni kam azalce ta kai ni ɗakin Ya Jafar, ashe Lawan yana laɓe a bayana ban san ya biyo ni ɗakin ba." Cikin haɗin baki duka suka ce, "Waye Lawan? "Mijin Fanteka ne." Uwani ta faɗa cikin kuka. "Ashe ba ki da hankali Uwani? Ashe sakarcin na ki da ake faɗa gaskiya ne? A ina Lawan ɗin yake kuma ɗan gidan uban waye a ƙauyen nan? Da har zai shigo cikin gida ya bi ki ɗaki." Baba Yunusa ya yi maganar rai a ɓace. "Ban gan shi ba Baba, duk neman da na yi ban gan shi ba ma ɗazu, kuma wallahi ganin idona ya fito daga ɗakin ya Jafaru. Sororo suka yi suka gagara gane kan maganar Uwani. "Shi Lawan ɗin ne zai ɓata a gidan kamar wani zobe? Kin san me kike faɗa kuwa Uwani?" Cewar Baba Mamman. Ganin duka ba su fahimci inda maganarta ta dosa ba ya sa Dada ta ce. "Lawan ɗin da Uwani ke faɗa ba kowa ba ne fa face zakaran da take kiwo, ko ba Lawan mai wake-wake ba Uwani?" Da sauri Uwani ta gyaɗa kai.   "Ba maganar zakara muka yi miki ba, muna magana ne akan tsakaninki da jafar." Baba Yunusa faɗa. Jin haka ya sa Uwani ta kwashe duk abin da ya shiga tsakaninta da Jafar ta faɗa musu, shiru duka suka yi Dada ta dubi Na madina ta ce. "Yaya wai haka ne abin da ta faɗa? Don gaskiya shedar zir haramun ce kar Mamman ya fusata ya ce mun yi wa ɗansa ƙazafi ya kaimu kotu, alƙali ya yanke mana bulala tamanin mu shiga uku." Jikin Na Madina ya yi sanyi don shi kasan ya san zargin ne yake yi idanunsa ba su gani ba. "Ni dai Allah Ya sani ban kama Jafaru da Uwani turmi da taɓarya ba, amma na ji waɗansu kalamai da suke yi a cikin ɗakin Kulun. Don Allah me zai sa su keɓe idan ba warware mutumcin sunna suke ba?" Sai a lokacin iyalan wurin suka fahimci gabaɗaya inda maganar su ta dosa. "Amma dai Yaya ka ci zarafin zuri'ata, yanzu saboda Allah wacce ƙiyayya kake yi wa Jafaru da Uwani da za ka nemi  ka haɗa su da hali irin ta'adar Iron Alto, ni dai ku zama shaida ta daga yau ba zan sake haɗa inuwa ɗaya da Yaya Musa ba." Dada ta yi maganar cikin kuka, ta mayar da kallonta wurin su Jafar ta ci gaba da cewa. "Ban da ƙarfin alƙawari ma me zai haɗa Uwani da Jafaru? Yarinya kyakkyawa kamar Uwani a ba ta Ɗansanda, Ɗansandan ma kamar Jafar mai zuciyar masifa. Ni tsorona ma kada watarana Uwani ta yi masa laifi ya sa bakin bindiga ya bindige ta..." "Allah ya tsare ni, ni kuwa me zan yi da Uwani wallahi ko a ƙafa aka ɗaura mini ita ba zan ja ba, kai ko abokina ba zan yi wa hanyar aurenta ba, haka kawai a ce na yi sanadin auren ƙazama kamar Uwani." Jafar ya faɗa a ƙazance kamar zai yi amai. "Idan kai ba ka so ba ai tuni alƙwari ya ba ka aurenta Jafaru, shafa Fatiha kaɗai ya rage muku. Amma fa wallahi faɗi kanka tsaye Jafaru ƙazantar uwani tun da na zo duniya ban taɓa ganin ƙazama irinta ba."  Jin tonan asirin da Dada take mata ya sa Uwani tura ba ki gaba. "Rigar mama wannan Uwani ba ta san ta canza ba sai dai idan na tilastata ta sauya, ban da ma Allah Ya kawo mu zamani yaushe yarinya za ta fara saka rigar mama a gaban iyayenta? To haka take zama da tsamin hammata, rannan ina kwance a saman kaina na ji tsami ya cika min hanci wallahi ina dubawa na ga ashe ɗan diras da kanfanta ne a ajiye. Ni ina tsoron ma kar a aurar da Uwani ta shafa wa Jafaru kwarkwata, don wallahi ko gorin kwarkwata aka yi wa Uwani sai haka. Amma dai tun da Hajiya Saro (Mahaifiyar Jafar) ta daina ƙazanta Uwani ma za ta daina, don bara war haka sai da na roƙa wa Uwani addu'ar yayewar ƙazantar nan a Harami." Dada ta mayar da kallonta wurin su Baba Rufa'i sannan ta cigaba. "Yanzu dai ba za mu tashi daga wurin nan ba sai mun kammala maganar yaran nan. Kun dai ga yadda Uwani ta zama budurwa ni tsorona ma kada ta fara baƙon wata a gabana na shiga uku..." "Subhanallah wannan wanne irin mummunan fata ne haka Kulu? Yanzu saboda Nasara ya gama wanke wa su Mamman hannu a ka sai su bar yaran nan haka?" Jafar ya saki murmushin takaici don shi gani yake duk sokiburutsun tsofaffin ne. "Don Allah ku dubi fuskar Jafaru washar yadda yake sakin murmushi, ko wannan miskilancin da yake yi fa aure yake so, kuma yanzu ya samu an soso masa wurin da yake yi masa ƙaiƙayi." Na Madina ya ƙarasa maganar yana sakin murmushi. Baba Rufa'i ya yi gyaran murya sannan ya furta. "Dada dama ba mu ƙi ta ku ba, amma gaskiya shekarun Uwani sun yi ƙanƙanta a aurar da ita yanzu Ina laifin ta gama sakandire ma..." "Sakandi me? Kana nufin zan zauna ina ganin Uwani a gabana har tsawon shekara biyar? Wallahi da kunci amanar zumunci, yanzu saboda kun ga ƙasa ta lulluɓe idon mahaifin yarinyar nan shi ne za ku watsa mata ƙasa a ido. Kaico mutuwa mai yankan ƙauna. Allah Ya jiƙanka Umaru, ni na san da Umaru ne ba zai taɓa yi wa bayanku haka ba." Shiru suka yi Baba Mamman na shirin magana Na madina ya katse shi, "Amfanin me karatun bokon zai yi mata? Aure fa shi ne sunnar Ma'aiki. Yanzu Dada ba ga su Safare nan ba kowacce tana ɗakinta da 'ya'yanta, ina ce firamare kawai suka yi. Ko kuma mu iyayenku da ba mu yi yi bokon ba sai a ce ba mu ji daɗin rayuwar aure ba?" Dada ta ware hannuwa cikin gamsuwa ta ce, "Gane mini hanya Yaya, so suke yadda fitsararrun yaran can suka rasa miji ita ma ta gandame mini a gabana." "Dada domin fa mu inganta rayuwar Uwani muke son mu tsaya mata ta yi karatu kamar yadda sauran yara suka yi, amma ba don wata manufa ba. Don Allah ku fahimce mu Uwani yarinya ce, har yanzu fa ba ta cika sha biyar a duniya ba duk fa girman jiki ne." "Ni dai Baba kawai a aura mini Ofisana, kar na je Furaira ta riga ni gabatar da kanta a wurinsa. Don wallahi Furaira masifar son shi take. Ka ga ni ma sai na dinga gayu irin nasa, Allah ko su Fanteke sai sun zama 'yan gayu..." Da sauri Jafar ya katse Uwani. "Ke ba na son shashanci da rashin hankali an gaya miki ni sa'anki ne? Tun wuri dama ki nemi mijinki don ni tuni akwai wacce zan aura a Lagos..." "Lagas? Yanzu Jafaru ka rasa wacce za ka auro sai ƙedarun Lagas, wallahi ni kam dole na je Zariya na samu Sa'idu." Dada ta faɗa cike da damuwa. "Jafar wannan daɗaɗɗan alƙawari ne da na ƙulla shi shi tun ranar da Uwani ta zo duniya, kamar yadda ka sani mahaifinta ya rasu tun tana ciki sakamkon hatsarin da ya yi. Ba ta taɓa sanin fuskar mahaifinta ba sai mahaifiyarta. Tausayinta ya sa na ɗauki alƙawarin aura maka ita matuƙar kuka kai munzalin aure, tun da a lokacin ba ka fi shekara goma sha uku zuwa sha biyar a duniya ba. Daga kai har ita mu muke da iko a kanku babu wanda ya isa ya bijire wa umarninmu." Baba Mamman ya yi wa Jafar jawabi fuska a haɗe. Dada ita da na Madina suka washe baki cikin farinciki ya ce, "Wallahi ka jima ba ka faranta mini rai irin na yau ba Mamman." "To yanzu dai duk ba wannan ba, abu ɗaya zan yarda da shi. Ba zan zuba wa Uwani ido ba a yi mata aure ba har nan da shekara biyar ba. Watan Maulidin nan me zuwa ne bikin su Shukra ko?" Baba Mamman ya gyaɗa mata kai. "Nan da watan maulidi nake son a ɗaura musu aure idan ya so nan da wani lokaci sai a yi maganar tariya. Ko dai mutuwa na yi kafin lokacin na sauke nauyin da muka ɗauka, ko ba haka ba Yaya?" Dada ta furta tana kallon Na Madina, cikin gamsuwa ya amsa mata. Duk yadda su Baba Mamman suka so shawo kan Dada don ɗaga maganar fir ta ƙi amincewa. Don haka suka haƙura suka tashi daga taron, Jafar tun ba su kai ga tashi ba ya fice fuuu daga ɗakin. Ganin haka ya sa Malam na Madina ya saki murmushi ya furta. "Ja'irin yaro wannan doron da ya yi yana yin aure zai miƙe, na san yau kwanan farinciki zai yi yoo aure wasa ne." Dada ta bushe da dariya. 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA BAKWAI Kamar Jafar zai tashi sama haka ya nufi sashen mahaifiyarsa saboda ɓacin rai ko gabansa ba ya gani sosai, da ƙarfi ya doka ƙofar falon Mami da su Shukra na zaune. A zabure duka suka miƙe Mami ta dube shi ta ce. "Hankalinka ɗaya kuwa Jafar? Saurin me kake yi haka?" Jafar bai tanka mata ba ya wuce kan kujera ya zauna yana furzar da iska mai zafi. Sai da ta ƙare masa kallo sannan ta ƙarasa kusa da shi ta furta. "A kullin ina gaya maka ka dinga rage wannan baƙar zuciyar taka. Me aka yi maka?" "Mami me ya sa Daddy ba ya son farin cikina ne?" Shi ma ya jefa mata tambaya. "Me ya sa ka faɗi haka?" "Yanzu Mami da girmana ni ba ƙaramin yaro ba a ce za a wani nemar mini matar aure, saboda Allah an yi mini adalci kenan? Atleast ko shawarata ai sai a nema." Nan take Mami ta haɗe fuska sai da ta sauke ajiyar zuciya ta furta. "Ina tunanin dai wasa yake yi maka, amma kuma ban da abin ka Jafar ka sani ko 'yar manya ce ita ma. Duk da dai na san kun gama daidaitawa da Safna ai ita ma wannan sai mu ji waye ubanta." Tun da Mami ta fara magana wani ƙululun baƙin ciki ya tokare masa maƙoshi, "Mami ko 'yar gidan uban waye ni fa idan ba na sonta ba zan aure ta ba. Kuma Daddy ya rasa wa zai haɗa ni da ita sai waccen kucaka, sakarya kuma ƙazamar yarinyar can Uwani." A zabure Mami ta miƙe tsaye har ba ta san lokacin da wani ashar ya suɓuce mata ba. "Uban waye zai haɗa ka da wata Uwani? Yarinyar da ko a mai aiki ba zan ɗauke ta ba. Ba zai taɓa yuwu ba wallahi, wannan ma ai shiga haƙƙi ne ina kai ina wata jakar yarinya Uwani." Jin haka ya ƙarfafa gwiwar Jafar nan ya kwashe duk yadda aka yi ya sanar mata, tun ba ta gama jin jawabinsa ba ta dakatar da shi tare da faɗin. "Bari na je na samu Dada wallahi ba zai taɓa yuwu ba wankan kuturu da sabulu." Fuuuu Mami ta wuce su Shukra na daskare mamaki ya mamaye su. "Waye haka mai ƙirar samudawa ya yi mini gandandan a tsaye?" Dada ta furta tana ƙare wa Mami kallo da ta yi tsaye a bakin ƙofa. Mami ba ta amsa ba ta wuce ta zauna a kan hannun kujerar Dada, tana cika tana batsewa. "Sannu da gida Dada." Mami ta furta a daƙile. Dada ta bi ta da kallo sai da ta taɓe baki sannan ta ce. "Sannunmu dai." "Dada a gaskiya ba a yi mini adalci ba, saboda Allah wai a rasa da wa za a haɗa Jafar sai da wata Uwani. Yaron nan fa namiji ne ko mace ba za a yi wa dole ba, gaskiya a duba lamarin nan don ko kaɗan ba su dace ba. Wai Jafar ne da Uwani yarinyar da ko wanka ba ta yi, ga rashin nutsuwa yarinya kamar rainon gwaro, ko tashin gidan mahaukata." Mami ta yi maganar tana haki. Baki sake Dada ta bi Mami da kallo har ta gama jawabi sannan ta ce. "Uwata kin gama magana ko da saura? Ke Saro amma dai ba ki da kunya kuma ko kaɗan ba ki da mutumci, yanzu ni kike gaya wa haka?Maganar auren yaran nan tamkar yau kika san da ita? Ina ce tun ranar da Uwani ta zo duniya aka ajiye ta. Ki saurare ni da kunnen basira, wallahi ko mutuwa na yi ban amince su Mamman su aura wa Uwani wani mijin ba Jafaru ba. Ke har kya yi zancen ƙazanta Saratu? Kin manta lokacin da kike fama da tsamin kai da na hammata? Ko kin manta lokacin da Mamman yake tasa ki zuwa banɗaki da soso ya tilasta miki ki yi wanka?" Mami ranta ya yi ƙololuwar ɓaci, a fusace ta ce. "Koma dai mene ne ni na ɗauki cikin Jafar na haife abina, don haka babu wata ƙatuwa da ta isa ta yi mini iko da shi wallahi duk ƙarfin ikonta..." Cikin sauri Dada ta katse ta. "Iyeee rashin kunya za ki yi mini Saro? To ni kuma ni na haifi Mamman kuma zan nuna miki ƙaryar gadarar da kike yi. Wallahi idan har ni na ɗauki cikin Mamman wata tara na haife shi sai an ɗaura auren Jafar da Uwani a yau, idan kin isa ki sa Jafar ya warware shi a yau ɗin nan kema." Dada ta ƙarasa maganar cikin ɓacin rai. Mami ta miƙe tsaye jikinta har rawa yake saboda ɓacin rai ta ce. "Ke kin haifa kuma kin isa ki yi gadara da ɗanki to wallahi ni ma zan nuna miki Jafar ba rainonsa na yi ba, naƙudar abina ni ma na yi na haifa don haka mu zuba mu gani." Daga haka Mami da buga wa Dada cinya haɗe da tsaki ta fice daga ɗakin. Daidai lokacin da Mami za ta fita Uwani ta kawo kai, duk da Uwani ba wani shiga sabgar Mami take ba amma ganin ta ya sa ta ce. "Ina wuni Mami." Ko ƙurar da ta ajiye Uwani Mami ba ta kalla ba ta wuce sashenta, Uwani ta taɓe baki ta faɗa ɗakin Dada. Tana shirin yin magana Dada ta katse ta. "Ke Kulu maza je ki kira mini Mamman shi da 'yan uwansa." Jin yadda Dada ta kira sunanta da Kulu ya sa ta sha jinin jikinta don ta lura ran Dada ya ɓaci sosai. Kai tsaye Uwani ta wuce sashen su Mami da sallama ta shiga ɗakin sai dai gaba ɗayansu babu wanda ya tanka mata, sai ma wani kallon tsana da suke bin ta da shi. "Dada ta ce Baba Mamman ya zo." "Sai ki neme shi a ɗakin uwarki." Mami ta furta. "Uwata fa? Me na yi miki za ki zage ni?" "To ko za ki rama ne? Mami ta katse ta. "Ba zan rama ba amma wallahi kada ki sake zagina ban yi miki komai ba, don uwa ba ta fi uwa ba..." Kafin ta rufe baki Shukra ta sauke mata tagwayen mari biyu a fuska. "Rashin kunya za ki yi wa Mami don ubanki, shegiya ƙazama baƙa mai baƙar aniya." Uwani riƙe da kumatu ta ce. "Kan uba marina kika yi?" Uwani na cikin magana Shukra ta sake sauke mata wani marin a fuska. Jin zafin marin ya sa Uwani ta yi tsalle sai ji kake tass a fuskar Shukra Uwani ta rama. Cikin ɓacin rai Mami ta fisgo Uwani da ƙarfi, ita kuma Shukra ta yi mutuwar tsaye tana mamakin marin da Uwani ta yi mata. Kamar haɗin baki Mami da Shukra suka rufe Uwani da duka tun tana ihu tana kuka har ta ja bakinta ta yi shiru saboda galabaita, sai da suka gaji don kansu sannan Mami ta koma kujera tana haki. Shukra na kan Uwani Daddy ya shigo cikin gidan, ganin irin dukan da take yi wa Uwani ya sa Daddy ya ɗauke Shukra da mari. Da kansa ya ɗago Uwani lokaci ɗaya fuskarta har ta sauya saboda kukan da ta ci. Ya lallashe ta sosai sannan Uwani ta faɗa masa saƙon Dada, a haka ta fara dafa bango ta wuce wurin Dada. Shi ma Dadday bai tsaya bi ta kan su Mami ba ya rufa wa Uwani baya. Ganin a yanayin da Uwani ta koma ya sake ɓata ran Dada, nan take ta sa Baba Mammam ya kira mata sauran 'yan uwansa. Suna zama ta wassafa musu duk abin da ya shiga tsakaninta da Mami, ta kuma nuna musu Uwani da irin dukan da suka yi mata. Daga ƙarshe ta ɗora da jawabin ɗaurin auren su Uwani a ranar, duk yadda suka so shawo kan Dada a kan a bari zuwa nan da watan Maulidin ma fir ta ƙi yarda. Sai ma ta nuna musu ana idar da sallar Isha'i su tabbata da sun ɗaura wa Uwani da Jafar aure. Dada ta dubi Baba Mamman ta ce. "Kai Mamman tun da ka zama sakarai sai ka bari Jafaru ya saki Uwani tun da uwarsa ta yi rantsuwa ba zai aure ta ba, to ka sani matuƙar Jafaru ya saki Uwani wallahi sai dai ka nemi wata uwar ba ni ba. Kuma a take kai ma ka miƙa wa Saratu takardarta ta saki. Na gama magana ku tashi ku ba ni wuri." Babu wanda ya iya tankawa haka suka fice ɗaya bayan ɗaya kowa zuciya babu daɗi. Uwani tun da ta kwanta zazzaɓi mai zafi ya rufe ta har sai da Dada ta ba ta magani ta sha, don haka da dare ko fita wasan dare ba ta yi ba. A ɓangaren Jafar ma tun da ya tashi daga falon Mami ya biya wasu almajirai suka gyara masa ɗaki, tun da ya shiga ɗakinsa sallah ce kaɗai take fito da shi. Daddy kuwa ko da ya fito daga sashen Dada sun jima suna tattaunawa da 'yan uwansa sannan kowa ya kama gabansa. Lokacin da aka idar da sallar Isha'i a masallacin gidan marigayi Mai shanu har mutane za su fara watsewa, malam Liman ya yi shelar akwai ɗaurin aure da za a yi. Nan take aka gabatar da waliyai daga kowanne ɓangare, aka ajiye sadaki dubu ɗari da hamsin da alewar ɗaurin aure. Jafar da ke can kusurwar bango da mamaki yake bin malam Liman, a zuciyarsa yake ayyana wanne irin aure ne za a ce za a ɗaura shi da daddare? Ganin su Daddy a gaba-gaba ya sa gabansa ya yi mummunan faɗuwa, ya yi saurin kawar da tunanin da ya faɗo masa a rai har yana neman tsari da shi. Wayarsa ya ɗauko ya fara latsawa, saƙon Safna ya ci karo da shi yana shirin buɗewa ya ji Liman ya furta. "Ga waliyin Jafaru ga waliyin Hauwa kulu an kawo sadaki dubu ɗari da hamsin lakadan ba ajalan ba. A bisa duka shaidun da ake buƙata sun kammala kowa ya shaida an ɗaura auren Jafar Mamman mai shanu da amaryarsa Hauwa kulu Umaru mai shanu, a kan sadaki naira dubu ɗari da hamsin lakadan ba ajalan ba." Daga haka ya fara rattabo addu'o'i ana ta saka albarka. Baba Isuhu ya ƙarasa yana yi wa Jafar Allah sanya alheri, ganin shi ne angon waɗanda ba su san shi ba suka ƙarasa suna masa fatan alheri. Tamkar butum-butumi haka Jafar ya ƙame a wuri ɗaya, ta cikin hayaniyar mutane ya sulale kai tsaye ya wuce gida. Na Madina sai ƙwala masa kira yake amma ya yi banza da shi, Jafar kai tsaye ɗakinsa ya shige ya datse yana kai wa da kawowa. "Ga alewa da dabinon ɗaurin auren ɗanki, ki saka albarka domin addu'arki na da muhimmanci a wurinsu. Bayan mun idar da sallah aka ɗaura auren Jafar da Uwani." Daddy ya furta wa Mami bayan ya shiga gida. A fusace Mami ta suri ledar dabinon ta yi wulli da ita, cikin ɓacin rai ta furta. "Daddyn Jafar yanzu tozarcin da za ka yi mini kenan? Wannan tsinannan auren zan saka wa albarka? Wallahi a daren nan sai Jafar ya saki Uwani." Murmushin takaici Daddy ya yi ya ce. "Na riga da na gama magana da Jafar, ki sani idan kika tilasta shi ya saki yarinyar nan wallahi sai na sauke miki igiyar aurenki uku daga kaina." Baki sake Mami ta bi Daddy da ya wuce ɗakinsa da kallo, saboda takaici sai kawai ta fashe da kuka. Su Shukra ne suka ƙarasa suka fara lallashinta. Cikin ƙanƙanin lokaci garin ya ɗauka 'Yar ƙashin gwiwa ta yi aure, wasu masu ƙarfin halin har gidan suka shiga yin tsegumi. Uwani duk wainar da ake toyawa ba ta sani ba sai daga baya Dada take sanar da ita, babu wani abu da ya ɗaga mata hankali abin da ya fi damunta ciwon jikin dukan da su Mami suka yi mata, wanda ta ci alwashin gabaɗaya za ta ladaftar da su ɗaya bayan ɗaya. Washegari ne ya kama sunan gidan Baba Isuhu sai dai tsamin jikin da Uwani take fama da shi ya hana ta walwala, don ta ci burin ko yaya ne ta tarwatsa 'yan taron suna. Yamma liƙis Uwani da ƙawarta Kubra na tafe suna hira Kubra ta ce. "Oh 'Yar ƙashin gwiwa yanzu dai aurenku da Ɗansandan nan ya tabbata, to kema 'yar sanda za ki zama?" Uwani ta yi jim sannan ta ce. "Da dai tuƙin jirgin sama nake son koya na dinga lulawa a jirgi ta cikin gajimare, an ce fa idan ka na jirgi har taɓo gajimare ana yi da hannu idan aka zira hannu. Amma dai yanzu tun da na auri Ɗansanda gaskiya ina jin ni ma 'yar sanda zan zama, ko ba komai Yaya Jafar ba zai mini baraza da bindiga ba tun da kar ta san kar..." Maganar Uwani ta maƙale sakamakon hango Shukra da saurayinta a ƙofar gida, suna jingine a jikin mota Shukra sai karairaiya take masa tana fari, a can gefen wata bishiya ta hango wani mahaukaci da ake yi masa laƙabi da 'Ba ka da nauyi.' Ɗabi'arsa ce ya ɗauki mace ko namiji ya dinga yawo da kai a gari yana ce wa ba ki da nauyi, kuma ba zai dire ka a ko ina ba sai tsakiyar kwata. A fili Uwani ta sheƙe da dariya Kubra ta ce. "Lafiya kike dariya 'Yar ƙashin gwiwa?" Gyaɗa marau ɗin hannunta ta kalla sannan ta ce. "Zo mu je wurin ba ka da nauyi." Kubra ta zaro ido, da sauri Uwani ta haɗe fuska. "Malama tsaya a nan wallahi kika ɓata mini shiri sai na sa shi ya ɗauki Baffanki gobe." Kubra ta ja baki ta tsuke don ta tabbata Uwani za ta aikata fiye da haka. "Baka da nauyi za ka ci gyaɗa marau?" Uwani ta faɗa tana kaɗa ledar gyaɗar a gaban mahaukacin. Washe baki ya yi cikin katuwar muryarsa ya ce. "Anci gyaɗa." "To bari kaji ina da gyaɗa marau soyayyiya da yawa, idan kana son na baka to ka ga waccen saurayi da budurwar ka je ka ɗauki budurwar ka zaga gari da ita, duk wanda ya zo cetonta ka haɗa masa jini da majina ni na sa ka. Na maka alƙawari zan ƙara maka wata, ƙila ma ba baka kwano guda..." Tun Uwani ba ta gama magana ba, Baka da nauyi ya fisgi ledar gyaɗar hannunta ya saka a aljihu, kai tsaya ya nufi wurin su Shukra ya tsaya a gabansu yana sakin shashashar dariya. A yatsine Shukra ta dube shi ganin yadda kayan jikinsa suke duƙun-duƙun ya sa Shukra ta tsartar da yawu sannan ta ce. "Malam mene ne haka ka zo ka saka mutane a gaba? Haka kawai ka saka mu tashin zuciya, dalla matsa daga nan." Ta yi maganar a yatsine ita a dole ta yi birga a gaban Salim. Salim ya kaɗa mukullin motarsa yana shirin yin magana sai gani ya yi Baka da nauyi ya suri Shukra yana dariya, da mamaki Salim ya dube shi fuska a haɗe ya ce. "Kai Malam wannan wane irin iskanci ne..." Tun Salim bai rufe baki ba Ba ka da nauyi ya sa gwiwar hannunsa, ya yi masa mahangurɓa a fuska ya kusa haɗa masa jini da majina. Wani haske Salim ya gani ya gifta masa kansa ya yi wani irin nauyi dum. Cikin gigita ya faɗa cikin gidan da gudu, da yake sashen Dada shi ne yake kallon ƙofa da sauri ya faɗa ciki a guje cikin fitar hayyaci, Dada na tsaye da ɗaurin ƙirji za ta sauya kaya sai ganin mutum ta yi ya shigo a guje yana wuri-wuri da wawure-wawure. "Hasbunallahu wa ni'imalwakeel kai wane gansamemen ƙaton ne haka..." Kalaman Dada suka maƙale sakamakon jin Salim na fisgar zanin jikinta ta ƙasa yana tura kai don shi maɓoya yake nema. "Kai don ubanka ba ka ganin ni tsohuwa ce, wai me kake nema a ciki ne?" Salim ya sake hankaɗe kansa yana shirin bankaɗe Dada ta faɗi a ƙasa, ganin haka ya sa Dada ta saka kuka tana faɗin. "Yau wane salon kwartanci ne haka ido biyu tun dare bai yi ba." Dada ta furta tana fisgar zanin shi ma Salim yana ja. Ganin Salim da gaske tura kansa yake yana yunƙurin sauke zanin Dada a ƙasa ya sa ta fasa ihu tana faɗin. "Jama'a ku kawo mini ɗauki ku ceci tsohuwa a hannun kwarto." "Don Allah ki ɓoye ni zai sauke mini fuskata daga jikin kaina." Salim ya faɗa cikin tashin hankali, yana sake fisgar zanin Dada yana tura kansa ciki. "Don Ubanka ka rasa a ina za ka ɓoye sai a cikin zanina, kai amma dai yau Allah Ya haɗa ni da lalatattun kwaratan zamani." Salim bai bi ta kan Dada ba ya sure zanin jikinta ya yi uwar ɗakinta a guje, sai ga Dada daga ita sai ɗan tofi shi ma ya zazzago ƙasa saboda kiciniyar da suka sha da Salim. Shukra ban da ihu da zille-zille babu abin da take yi, don Ba ka da nauyi ya sauke ta amma ya ƙi, yara kuwa sai bin su suke a guje suna masa waƙa da tafi. Wannan ya sake ingiza shi ya ci gaba da gudu da Shukra a saman kansa, ɗankwali da mayafinta tuni suka cire tun a ƙofar gida. Sai da ya gaji don kansa ya je wata ƙatuwar kwata ya tsoma ta a ciki. "Allah Ya isa tsakanina da kai." Shukra ta furta cikin kuka. Hannu ya zira a aljihu ya ciro wata ƙatuwar goruba ba ta yi aune ba sai ji ta yi ƙwal ya buga mata a goshi, ya juya ya ci gaba da tafiya. Azaba ta sa Shukra ta rushe da kuka, ga zurfin kwatar ya mata nisa ba za ta iya fitowa ba ga zafin dukan goruba a goshi. Kafin wani lokaci tuni goshinta ya yi wani malolo a daidai wurin da ya ƙwala mata. Cike da takaici Dada ta rushe da kuka sannan ta ce, "Jama'a ku zo ya ƙwace mini zanin jikina, ku kawo mini ɗauki kwarto har uwar ɗakin tsohuwa." 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA TAKWAS Uwani saboda dariya har kwanciya ta yi a ƙasa, Ba ka da nauyi ya ƙarasa wurinta tun bai yi magana ba ta miƙa masa ɗayar ƙullin gyaɗar. "Ba ki da nauyi ta yi malolo." Haka yara suka dinga yi wa Shukra waƙa suna tafi, ban da kuka babu abin da take yi saboda tsananin kunya da ɓacin rai. Da ƙyar wasu matasa suka kori yaran suka yi kama-kama suka tsamo ta a cikin kwata. Tana tafe ruwan kwata na ɗiga wasu daga cikin yaran suka fara yi mata wata waƙar. Ɗoyi, ɗoyi ɗoyi. Ɗoyi damalma kashi. Ɗoyi tukunyar kashi. A haka Shukra ta ƙarasa gida nan ma wasu daga cikin tsurarin yara suka bi ta Uwani na take musu baya, Shukra na shiga sashensu ta ɓarke wa Mami da wani irin kuka. "Yaya Shukra lafiya? Me ya same ki a goshi? Mene ne wannan yake wari a jikinki kamar kwata? Ina shi Yaya Salim ɗin?" Auta ta jero mata tambayoyi, sai dai babu ɗaya da ta iya amsawa ban da hawaye da ke shatata a fuskarta. Mami da Auta suka taimaka mata ta gyara jikinta sannan ta faɗa musu abin da ya faru, suka shiga zagin Ba ka da nauyi suna mamakin in da Salim ya je bayan motarsa na ƙofar gida. Jin ihun Dada ya sa su Atika shiga sashenta da sauri, ganinta a daskare daga ita sai ɗan tofi ya ba su mamaki domin Dada ba ta taɓa sauya kaya a gaban mutane. "Dada lafiya?" Hannu na rawa ta nuna uwar ɗakin. "Wani tabbataccan kwarto ne ya fisge mini zani ya yi uwar ɗaki. Ni Kulu ban san uwar me zai laluma a jikin tsohuwa ba." Da sauri su Atika suka leƙa ɗakin, ba su iya hango komai ba sai 'yan idanun Salim da ke duƙe a ƙarƙashin gado. Fa'iza ce ta kira Baba Isuhu, da sauri ya ƙarasa hannunsa ɗauke da ƙatuwar gora ya fisgo Salim. Sai dai sororo ya yi yana bin yadda halitar fuskar Salim ta sauya. "Wa nake gani kamar Salim? Kai uban me ya kai zanin Dada hannunka?" Salim da gefen baki zuwa fuskarsa ya kumbure sundundun ya ce, "Baba wani mahaukaci ne zai sauke mini fuska don Allah ku ɓoye ni. Ya ɗauke Shukra a ka ma ya tafi da ita." Sai a lokacin suka fahimci wurin da maganar Salim ta dosa, Baba Isuhu ya miƙa wa Dada zaninta. Ya kama hannun Salim suka fice Salim sai tirjewa yake, a zuciye baba Isuhu ya waigo ya furta. "Me kake yi haka ne wai? Ka san Allah ka ci sa'a na gane kayan jikinka don mun gaisa ɗazu kana ƙofar gida, wallahi da don ta wannan sukunbiyar fuskar taka ne ba zan gane ka ba. Dubu fa yadda ka koma fuska kamar ta sumammiyar akuya. Mu je na raka ka ƙofar gida ka tafi don indai Ba ka da nauyi ne fiye da haka ma zai yi maka." Sai a lokacin Salim ya saki jiki suka ƙarasa, da sauri ya shige mota ya fusge ta da gudun gaske ko waige ba ya yi. Su Dada suna tsaye suna mayar da yanda aka yi wayar Dada ta fara ringing, da sallama ta ɗauka jin muryar Maryama mahaifiyar Uwani ya sa ta furta. "Ke kuwa Maryama da ƙuruciyarki amma waya ta nemi ba ki wuya, tun daren jiya nake kiranki na sanar da ke abin alheri amma waya a kashe." Maryama cikin shasshekar kuka ta ce. "Dada hankalina ne ba a kwance ba." "To Allah ya rufa asiri ai ni dama tun da na ga yanayinki na san Aramma na zalintarki, ki ci gaba da haƙuri Maryama komai ya yi don kansa." Maryama ta saki kukan da ke cinta, Dada na son Maryama shi ya sa duk lokacin da suka yi waya take tausarta. "Kin ga ki yi shiru 'yar nan su maza fa haka suke, ni tsorona ma kada Aramma ya zo ya ji kina mini kuka ya ce ko Umaru kika tuno. Yanzu dai ba wannan ba jiya da dare dai an cika alƙawarin da aka ɗauka, Uwani dai an ɗaura aure ita da Jafar. Abin ne ya zo a gaggauce, amma dai tariya sai nan da watan maulidi." Maryama ta ji daɗi don ta san waye Baba Mamman, amma har a ranta ta so a ce Uwani ta yi hankali kafin ɗaurin auren. Sai da ta kwararo addu'a sannan ta sanar da Dada dalilin kiranta. "Dada dama kiranki na yi na faɗa miki Me sunan Iya ce ta rasu (Babbar 'yarta ta gidan Aramma.)" Salati Dada ta rafka sannan ta yi mata gaisuwa ta kuma yi mata alƙawarin washegari za su shiryo su zo mata gaisuwa. Bayan sun gama waya Dada ta miƙa wa Uwani waya, suka gaisa sannan ta yi masa sallama. Kimanin ƙarfe goma na safe su Dada suka isa ƙauyen da mahaifiyar Uwani take aure, sun yi kara sosai don har su Baba Yunusa gabaɗaya suka je mata da matansu. Tun da suka faka motoci yara ke zuwa kallonsu, mazan suka zauna a tabarmar da ke ƙofar gida suka tambayi mijin Maryama aka ce musu ya shiga cikin gida. Su Dada kuma suka shiga ciki. "Gata nan da ran Allah ita ta san inda ta kai mini yarinya aka cinye ta, amma idan ta zauna ta ishi mutane da kukan munafurci. Daga zuwanta garinsu ta dawo da yarinya ba lafiya, wai muna zuwa aibitin gangare da suka tura mu babban asibiti a binni aka ce sikila ce, yo ban da ƙaryar likitoci lokacin iyaye da kakanni aka san wata sikili? Ta kai mini yarinyar dai mayu sun cinye kawai." Shigar su Dada gidan suka samu Aramma na zazzaga wa Maryama masifa yana kumfar baki, tana durƙushe a gefen yayan Aramma da ya zo yi mata gaisuwa. A lokacin Aramma ya zo wucewa ya shi ne yake yi mata sababi. Ganin su Dada da yanayin shigarsu ya sa ya hau yashe baki. "Barkanku da zuwa Hajiya." "Barka dai." Dada ta amsa a daƙile. Jin muryar Dada ya sa Maryama ta miƙe tana goge hawaye ta shiga yi musu sannu da zuwa. "Ai kuwa wannan mutumin sai na gyara maka zama." Uwani ta faɗa a ranta. Maryama jiki a sanyaye ta miƙe za ta wuce da su ɗaki. "Ke Maryama wanne irin rashin hankali ne haka kina ganin baƙi ba za ki kai su ɗaki ba." Aramma ya faɗa cikin faɗa shi a dole sai ya birge su Dada. Ɗaki ta kai su bayan sun gaisa suka yi mata gaisuwa cikin jimami, Dada har cikin ranta ba ta ji daɗin irin zaman da Maryama take yi da Aramma ba, domin mace ce mai sanyin hali da haƙuri. Duk wanda ya santa idan ya san Uwani dole zai ce albasa ba ta yi halin ruwa ba. Aramma jikinsa har rawa yake ya sa aka sayo musu ruwa, ba su jima sosai ba Dada ta kawo kuɗin sadaka dubu biyar ta bata. Sauran sirikan Dada kuma mai ɗari biyar mai dubu ɗaya duk suka haɗa mata, lokacin da za su tafi ne Dada ke ce wa Maryama Uwani za ta zauna har sai an yi sadakar uku za ta tafi. Har ƙofar gida Maryama ta raka su, su Baba Idris suka yi mata gaisuwa, suma suka kawo abin sadaka suka ba ta da shi ma Aramma. Har sun ɗauki hanya za su tafi Dada ta dawo ta ja Maryama gefe tana yi mata raɗa. "Dama kuɗin da aka ba ki ko da wasa kada ki ba wa wannan mijin naki kin ji Maryam!" Maryama ta gyaɗa kai jiki a sanyaye sannan ta raka Dada bakin mota tana ɗaga musu hannu. "Dada gaskiya zan yi kewarki kwana biyu an ya ba biyo ku zan yi ba?" Uwani ta faɗa tana tura ba ki gaba. Dada ta watsa mata harara sannan suka wuce. Tun da suka koma cikin gida Uwani ta lura da mahaifiyarta sam ba ta da nutsuwa, suna nan zaune sai ga Aramma ya shigo. "Ke Maryama kawo abin sadakar nan da aka ba ki zan haɗa a yi abincin rana." Tamkar kazar da ƙwai ya fashe wa a ciki haka Maryama ta miƙe jiki ba ƙwari ta kunto kuɗin wurin su Baba Idris ta miƙa masa. "Ke ba na son shashanci da rainin hankali, kina nufin su matan ba su ba ki komai ba? Wai Maryama me ya sa kin fiye baƙin halin tsiya ne." Ran Maryama ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, ganin irin tozarcin da Aramma yake yi mata a gaban Uwani da kuma sauran mutanen da suka zo gaisuwa. Don haka rai a ɓace ta ce. "Wai Aramma ya kake so na yi ne? Me ya sa..." Tun ba ta gama magana ba Aramma ya ɗauke ta da mari, yana shirin kai mata duka Uwani ta shiga tsakaninsu ta furta. "Baba bari na miƙo maka kuɗin a cikin jakar can ta ajiye dama na ji ta ce za a auno garin masara a yi tuwo, amma bari na miƙo maka." Jin haka ya sa Aramma ya washe baki ya ce. "Ka ji yarinya mai hankali maza miƙo mini, ke dai kin yi asarar hali Maryama." Babu musu Uwani ta zuge jakar da ta ga mahaifiyarta ta zuba kuɗin a ciki, ta ɗebo su duka ta miƙa masa. "Kai Allah wadaran naka ya lalace wallahi Maryama kin ji kunya ace wai har 'yar cikinki ta fi ki hankali." Wasu daga cikin ƙannen Aramma suka bi mahaifiyar Uwani da baƙaƙen maganganu. Ba ta tanka musu ba sai ma ruwan hawaye da ke tsiyaya daga fuskarta. Uwani na daga gefe ta ci gaba da kallonsu ɗaya bayan ɗaya, kowanne tana zana gashin azabar da za ta yi musu daga baya. Sai da mutane suka ragu a ɗakin sosai daga Maryama sai 'yan uwanta ta dubi Uwani ta ce. "Me ya sa za ki ɗebi kudina ki ba shi." Ta ƙarasa maganar fuska a haɗe. "Gobe da safe zai dawo miki da su Inna rance na ba shi!" Uwani ta furta cikin rashin damuwa. "Rance fa? Ta ya ya zama rance bayan a kan idona kika ba shi?" "Allah Inna kada ki damu zai dawo miki da kuɗinki har ma ya ƙara miki wasu." Jin sokiburutsun Uwani ya sa Maryama ba ta sake bi ta kanta ba saboda takaici. "Maryama yaya aka yi kika bari har ya ga lokacin da aka ba ki kuɗin nan? Kin fa san halin mutumin nan sarai, ba shi da tausayi ko kaɗan." Indo kishiyar Maryama ta furta ƙasa-ƙasa. "Ai kin san tun da ya gan su ya san za su ba ni wani abu, kuma ragowar ma ba ni na ba shi ba yarinyar nan ce ta ba shi." Maryama ta furta. Suka gama jajantawa juna, don zaman da suke yi sam babu kishi a ciki saboda dukkansu ba wani daɗin zama da shi suke ji ba. Wuni ɗaya da Uwani ta yi a gidan ta fahimci irin zaman ƙuncin da mahaifiyarta da kishiyarta suke yi a cikin gidan, a kan idonta ta ga Aramma ya yo cefane har da nama ya ce a yi masa jar miya da shi. A yadda ta lura hatta abinci ma daban ake yi masa, su kuma duk kwamacalar da ya ga dama sai su dafa. Don abincin dare sai da ƙyar Uwani ta iya cin miyar kukar da aka kaɗa, saboda haka ta ci alwashin gyara masa zama kafin ta bar gidan. Tun da doshin magriba Uwani ta hangi wani ludayin silba a kwandon wanke-wanken mahaifiyarta, a fakaice ta ɗauke shi ta ɓoye sai da dare ya tsala kowa ya yi bacci sannan ta saci jiki a hankali. Har za ta fita ta hangi wani zumbulelen farin hijabin Inna Suwaiba, wani tunani ne ya faɗo mata da sauri ta saki murmushi. Ta figi hijabin a hankali ɗayan hannunta ɗauke da ludayin sulba, can hanyar soro ta nufa da yake a baki-bakin ƙofa turakar Aramma take, daga ɗakinsa kuma sai ɗakin da suke ajiye kayan abinci. Toka ta ɗiba ta bursune fuskarta da ita sannan ta saka zumbulelen farin hijabin, ta leƙa ɗakin ta hango Aramma a kwance ya sharɓe sai sakin munshari yake yi daga shi sai gajeren wando. Da yake irin mutanen nan gajeru masu ƙiba ga uban tumbi. Tana shiga ɗakin ta tsaya a kansa, sai da ta gimtse dariyarta sannan ta daidaici gefen goshinsa ta ba shi raaaal da ludayin hannunta. A firgice Aramma ya miƙe yana dafe da goshi, "Wane ɗan iskan ne a tsohon daren." "Tawagar fatalwar 'yan iskan lahira ne!" Uwani ta faɗa da wata irin murya, ta sa hannu ta cikin hijabin ta buɗa shi, sai ta ƙara faɗi ta cikinsa. A razane Aramma ya ja da baya ganin hallitar da ke tunkaro shi. "Mu sababbin ƙawayen 'yarka da ta baƙunci lahira ne. A cikin fatale ma mu tawagar shaiɗanu ne domin fatattaka ɗan adam muke yi da kulkin lahira. Ita da bakinta ta gaya mana irin zalincin da kake yi wa iyalinka, don haka muka zo domin mu tsintsinka hanjin cikinka, ko kuma mu gayyato 'yan uwanmu mu yi daga-daga da kai." Uwani ta yi magana tana wani miƙa wuya gaba. Jin kalaman Uwani ya sa Aramma ya fashe da wani irin kuka mai cin zuciya, cikin tashin hankali ya ce. "Ku dubi Allah ku yi haƙuri wallahi zan daina duk abin da nake yi..." Da sauri Uwani ta katse shi. "Zo nan maza-maza, matso nan." "Don Allah ku yi mini rai." Aramma ya faɗa fuska haɗe da hawaye da majina. "Za fa ka taka ɗan tsiti a bayanka, wallahi tawagarsa ta fi ta mu bala'i ka matso na ce maka." Da sauri Aramma ya matsa tiɓi-tiɓi sai haɗa gumi yake. Yana zuwa ya tsugunna a ƙasa, hannun Uwani mai ɗauke da ludayin da ke cikin hijabi ta ɗaga da sauri ta sake ba shi raaal a ƙeyarsa. A zabure Aramma ya miƙe sai da ya yi tsalle uku ya faɗi a can gefe cikin azaba. "Fatalwar 'yarka ta gaya mana duk abin da matanka suke samu karɓe musu kake yi, a jiya ma ka karɓe wa uwar marigayya kuɗaɗenta to ko ka mayar mata da abin ta ko kuma mu mayar da kai kuɗi. Domin muna cikin irin fatalwar da ke yi wa 'yan ƙungiyar asiri aiki, za ka zama kuɗi wayyo kuɗi, kuɗi masu daɗi." Uwani ta yi maganar tana wani tsalle tana ɗaga hannu ta cikin hijabi kamar mai shirin tashi sama. "Na rantse da Allah ko wasu aka ce na ƙara mata yanzu zan ƙara mata su." Uwani ba ta bi ta kansa ba ta ce. "Da ma ga hantarka da zuciyarka nan muna gani manya ne, ko su kaɗai muka tsaface za ta kawo mana miliyoyi." Da sauri Aramma ya dafe cikinsa da hannuwansa biyu, ya sake ɓarkewa da kuka. "Idan ka sake ka tona mana asiri wallahi a yanzu za mu hallaka ka." Jin haka ya sa Aramma ya haɗiye kukansa, ya sa hannu biyu ya toshe bakinsa. Uwani ta sake jingina da bango ta furta. "Ganin yadda muka ga ka yi nadama za mu ɗaga maka ƙafa na kwana biyu mu ga idan za ka sauya halinka, kuma ka gaggauta mayarwa da mahaifiyar 'yar uwarmu kuɗinta. Sannan ita da kishiyarta dole ne ka ƙara musu dubu hamsin-hamsin. Kuma ya zama wajibi duk sati ka dinga ba su dubu uku-uku na kashewa." "Duka na ji kuma na yi alƙawari zan yi yadda kuka ce, na gode muku Allah Ya biya ku." Aramma ya yi maganar yana rissinawa. "Ba ma buƙatar godiya, yanzu dai za mu tafi da kai ka je ka ga makwancin 'yarka, sai mu baro ka a can bayan sadakar uku sai mu dawo..." Tun Uwani ba ta gama magana ba ya katse ta cikin kuka. "Wallahi na haƙura da ganin ta, Allah ba sai na ga halin da take ciki ba. Na san mai sunan Iya tana da halin na gari." "To kuwa ya zama wajibi ka zaɓi ɗaya, ko mu ɗauke ka ta ƙarfin tsiya mu tafi da kai. Ko kuma ka zo ka ku yi sallama da shugabar tawagar 'yan iskan fatale." Jin haka ya sa jiki na rawa ya matsa gaban Uwani ya ce. "Zan gaisa da ita..." Maganar bakinsa ta katse sakamakon jin saukar ludayin da ya yi a gaban kansa. Wannan karon kasa motsi ya yi ganin haka ya sa Uwani ta sake sauke masa na biyu aka sannan ta ɗora da cewa. "Yanzu haka za mu fita mu ba ka wuri, sauran tawagarmu na tsakar gidan nan. Kuma duk abin da ka ji ko kuma duk hukuncin da ka ji muna aikatawa matuƙar ka leƙo to zai dawo kanka. Sannan saura idan gari ya waye ka ce ga abin da ya faru da kai." Daga haka Uwani ta fice tana wani shagiɗewa gefe tana tura wuya gaba. Kusan duk abin da ya faru tsakanin Uwani da Aramma, Yaya ƙarama da su Rahane 'yan uwan Aramma sun ji, sakamakon ɗakin da suke kwance a jikin na Aramma yake. Da yake dama idan wani abin taro ya kama a gidan to duka danginsa a wannan ɗakin suke sauka. Kowannensu na daga kwance cikinsa ya ɗuri ruwa ko motsin kirki babu mai yi, babban abin da ya ɗaga hankalinsu yadda suka dinga jiyo kukan Aramma ƙasa-ƙasa, da ita kanta saƙon fatalwar da take faɗa. Suna nan kwance suka ji motsin Uwani a ƙofar ɗakinsu tana ɗan wani gurnani, take fitsari ya jiƙe zanin Yaya ƙarama. Uwani na ɗaga labulen ɗakin ta hango yadda aka jere yara a ƙasa, ɗaya bayan ɗaya haka ta dinga jidar yaran tana kai wa tsakar gida. Yaya ƙarama na daga kwance ta ji Uwani ta dafa ƙafarta, jiki na rawa ta ce. "La'ilaha'illahu Muhammadur Rasulillah." "Ba za ki mutu yanzu ba sai mu fafe ƙwayar idonki." Uwani ta faɗa da wata irin murya, har ta juya za ta fita ta ce. "Su kuma waɗancan yaran zan ba wa ƙananan fatalenmu umarni su gama da su." Uwani na ƙarasa magana ta wuce wurin yaran da ke kwance a tsakar gida, idan ta ɗauko yaro ɗaya sai ta gasa masa mintsini ta tura shi cikin ɗaki. Ganin yadda yaran ke shigowa a firgice cikin kuka ga magagin bacci ga kuma zafin mintsini, ya sa su Yaya ƙarama suka banka uwar ɗaki a guje. Uwani ta yi wata irin sufa ta rufa musu baya tana faɗin. "Ya Ahalul fataleeee ku zo ga nama mun samu." 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA TARA Sai a lokacin Uwani ta fahimci ashe ba iya su Yaya Ƙarama ce kaɗai idonsu biyu ba, hatta mutanen da ke cikin uwar ɗakin lakur suka yi sai da suka ji Uwani ta yi sufa za ta faɗo uwar ɗakin suka fara ihun neman ceton rai. A daidai bakin ƙofar uwar ɗakin Uwani ta tsaya sai ta hango wata wuƙa a gefen randa, ta janyo ta ta fara wasawa. Naziru ɗan wurin Sa'a da a lokacin ya wartsake ya kafe Uwani da kallo, ganin haka ya sa Uwani ta kalle shi tana zare ido ta ce. "Ga wani ɗan ƙwage da shi za mu fara." Uwani ta ƙarasa maganar tana fusgar hannun Naziru da bai wuce shekara huɗu ba. "Wayyo Iyata! Wayyo Iyata." Ya fara ihu hankali a tashe don ƙiri-ƙiri ya ga wuƙar hannun Uwani. Sa'a na ganin haka ta fara jan hannun Naziru Uwani na jan ɗaya, Sa'a ta waiga wurin su Yaya ƙarama ta ce. "Ƙarama don Allah ku kawo mini ɗauki Naziri zai tafi." Yaya ƙarama da ke ƙuryar uwar ɗaki ta ce. "Sa'a ki haƙura da Naziru tun da ba wuce haihuwa kika yi ba, wallahi a yanzu ko Habibu (Shi kaɗai ne ɗanta) suka ja sai dai na bi shi da addu'a." Sa'a na shirin magana Uwani ranƙwala mata ludayi a ka, a guje ta saki hannun Naziru cikin kuka ta faɗa uwar ɗakin tana faɗin. "Wayyo Naziru." Shi ma Naziru sai tirjewa yake yana faɗin. "Iyata wayyo Iyata." Yaya ƙarama ce ta yi sauri ta banka ƙofar ɗakin ta danna sakata tana sauke ajiyar zuciya. "Idan kun rufe ƙofa za mu ɓullo ta ƙarƙashin ƙasa, mu dama ai daga kabari muke. A wannan lokacin babu buƙatar mu yi muku bayanin mu su waye, domin hukunta ku muka zo yi ɗaya bayan ɗaya, a kan cin zarafin da kuke yi wa mahaifiyar 'yar uwarmu da kishiyarta. Mu tawagar fatale sai mun saɓule fatar jikinku sannan mu tsotse romo da ɓargon jikinku. Amma za mu ɗaga muku ƙafa zuwa nan da ɗan wani lokaci, don mun lura kun fara nadama. Sai dai muna mai tabbatar muku babu wanda zai tafi gidansa sai an yi sadakar uku, idan kuma mutum ya yi kuskuren tafiya gida gobe, to a daren ranar sai dai ya kwana a ƙiyama." Uwani ta furta a lokacin da ta fita da Naziru tsakar gida da ke ƙwala ihu. A yadda ta lura kusan ilahirin mutanen gidan duka sun tashi, wata dabara ce ta faɗo mata don haka ta buga tsalle a tsakar gidan ta ce. "Waɗanda kuke leƙenmu muna gano ku, ke wato har da ke ko. Wallahi ɗaya bayan ɗaya za mu bi ku mu ƙwaƙwale idanunku idan ba ku koma kun kwanta ba." Ta saki hannun Naziru ai kuwa da gudu ya faɗa ɗaki yana ihu, sai ta tafi da gudu ta nufi ɗakin mahaifiyarta, a guje ta ji mutanen ɗakin suna shigewa uwar ɗaki wasu na hantsilawa. Nan ma ta nufi ɗakin kishiyar mahaifiyarta ta razana su, sai da ta tabbatar da sun gama tsorata kowa ya shige uwar ɗaki sannan ta lallaɓa ta isa banɗaki ta wanke fuskarta. Ta duƙunƙune hijabin Inna Suwaiba ta soke a hammata, sai da ta shirya sosai sannan ta nufi ɗakin mahaifiyarta da gudu tana faɗin. "Wayyo Allah! Ku taimaka mini za su ƙara janye ni." Tana shiga ɗakin ta tarar falon mahaifiyarta babu kowa an banke uwar ɗaki sai ƙananan yara da ke kuka suna buga ƙofa, saboda kada a gano Uwani ita ma ta fara bubbuga ƙofar tana ihu. Da ta lura ba za su buɗe mata ba sai ta janyo ƙofar falo ta datse. Har aka yi assalatu babu wanda ya yunƙurin fitowa daga ɗakin, duk da duka baƙin gidan a zuciyarsu kowa ya ayyana gari na wayewa tafiya zai yi. Amma da sun tuna kashedin da aka yi musu a kan kada wanda ya bar gidan har sai an yi sadakar uku sai jikin kowannensu ya yi sanyi. Sai da gari ya yi tangararan sannan Indo ta yi ƙarfin halin buɗe ƙofa, kamar sababin munafukai haka mutane suka dinga leƙowa ɗaya bayan ɗaya suna fitowa suna yin alwala suna sallah. Duk wannan abin da ya faru bayan da gari ya waye babu mutum ɗaya da ya jajantawa kowa, domin kowa a tsorace yake. Su Uwani suna zaune sai ga Aramma ya shiga ɗakin kansa ya yi waɗansu ƙulalai sun fi biyar, daidai tsakiyar hancinsa har wani ja ya yi yana maiƙo. Da mamaki suka bi shi da kallo, Aramma ya zauna daɓar jikinsa zafi zau da zazzabi. Gaishe shi mutanen ɗakin suka yi, suna son jin abin da ya faru da shi suna tsoro. Hannu ya sa a aljihu ya zaro kuɗin ya ce. "Ungo wannan Maryama, kuɗinki na jiya ne. Wannan kuma kyautar dubu hamsin ce na ba ki ita ma Indo zan miƙa mata nata." Baki sake Maryama ta bi shi da kallo, ta ce. "Malam dubu hamsin fa? An ya ba mantawa ka yi ba?" Aramma ya dube ta a fusace da ya tuna gargaɗin fatalwa sai ya wayance ya sassauta murya ya furta. "Maryama shaidar da za ki yi wa mijinki kenan? Kyautatawa ce kawai ta sa na ba ku." Maryama hannu na rawa ta sa ta karɓa tana zuba masa godiya, Aramma har ya miƙe zai fita Inna Suwaiba ta ce. "Aramma ungo shafa-shafa sai ka shafa a malolon nan na ka, Allah dai ya sawaƙe sanyi haka yake lokaci ɗaya ka ga wuri ya luluye. Ko kuma bige wa ka yi ne da dare?" Aramma da ba ya son a ja doguwar magana ya karɓa ya yi gaba ba tare da ya amsa mata ba, ɗakin Indo ya faɗa ita ma ya sallame ta ya koma ɗakinsa don ilahirin jikinsa ciwo yake masa. Aramma na shiga ɗaki sai ga Indo jiki na rawa ta shiga wurin Maryama suka fara tattaunawa cikin mamaki, ba su ƙara nutsa wa a tekun mamaki ba sai da suka ji Aramma ya ce a yi shinkafa da miyar dage-dage da rana. Wannan sabon sauyi da suka samu daga wurin Aramma ba ƙaramin daɗi ya yi musu. A na gobe Uwani za ta koma gida wurin ƙarfe goma sha biyu na dare ana zaune ana ɗan hira, ta hangi Aramma ya suri buta ya yi banɗaki. Sai da ta tabbatar da hankulan mutane ba ya kanta ta saci jiki ta nufi banɗaki, da yake banɗakin ya yi nesa da ɗakuna don haka ta laɓe a can kusurwar bango ta fara magana. "Baba ga tawagar 'ya'yanka sun dawo. Kada ka tsorata mune dai fatalen nan." Aramma da ke tsugunne a kan masai sai abin ya yi masa a daidai, saboda wata sabuwar gudawa ce ta tsarge shi. Gumi ya fara tsattsafo masa ya ce. "To 'ya'yana don Allah kada ku taɓa lafiyata, wallahi har yanzu ban warke ba." "Ba za mu sake cutar da kai ba, domin ƙawarmu wato matacciyar 'yarka ta ce ta ga irin kyautatawar da kake yi wa iyayenta da 'yan uwanta. Ki yi masa magana ya ji sabuwar muryarki ta cikin jinsin fatalwa." Uwani ta yi maganar tana wani fuffuka, sannan ta maƙale murya ta furta. "Baba ni zan tafi da kai na fi so na dinga ganinka." Tamkar an buɗe fanfo haka cikin Aramma ya birge, ya ci gaba da sakin gudawa babu ƙaƙƙautawa. Cikin tashin hankali ya ce. "Na yafe don Allah ki je ki ɗauki mahaifiyarki." "Shi kenan Baba zan dai dinga kawo muku ziyara a ɓoye duk dare ina ganin rayuwar da kuke yi, idan na ga saɓanin abin da ka fara yi wallahi cikin tumbinka zan shiga, na kannaɗe hanjinka ita kuma kodarka na fansarwa shugaba." Uwani ta furta tana gimtse dariyarta. "Wallahi komai zan ci gaba da yi idan na saɓa ki mini duk abin da za ki yi mini." "Mu zamu tafi Baba sai mun sake zagayowa." Uwani na gama faɗar haka ta fara wata fuffuka tana gurnani sannan ta saɗaɗa ta bar wurin. Saboda yadda Aramma ya razana bayan da ya gama uzurinsa a duƙe ya dinga tafiya, saboda yadda ya ji ƙafafuwansa sun yi sanyi har sun gagara ɗaukar nauyin gangar jikinsa. Ranar da aka yi sadakar uku dai tun da safe wasu daga cikin 'yan gaisuwa suka fara watsewa, domin dama wasu tamkar a kan ƙaya suke. Ita ma Uwani sai da aka yi sallar la'asar sannan Aramma ya zo ya sanar da Maryama an zo ɗaukan Uwani, ta so Uwani ta ƙara kwanaki amma babu yadda ta iya haka ta danne. Wasu daga cikin 'yan uwan mahaifiyarta sai tsokanarta suke suna amarya sai sun zo biki. Kafin Uwani ta fita sai da Maryama ta sata a gaba ta yi mata nasiha sosai. Fakare Uwani ta yi tana sauraronta kamar nasihar na shigarta, sai gyaɗai kai take tana amsawa. Sai da ta gama sauraron mahaifiyarsa sannan ta ce. "Ni kam Inna don Allah zan faɗa miki wata magana amma don Allah kada ki faɗa wa kowa." Take gaban Maryama ya faɗi amma sai ta basar ta ce. "Ina jin ki babu wanda zai ji Uwanina." Duk abin da ya faru tun daga farko har ƙarshe ta sanar da ita tana dariya, ita kanta Maryama dariya take sheƙawa sanna ta riƙe baki ta furta. "Allah Ya shirye ki Uwani ni dai wallahi ban san halin wa kika ɗauka ba, mahaifinki dai har ya fi ni sauƙin kai. Allah Ya shirya ki ko ba komai kin samar mana 'yanci." Suna cikin haka suka ji ƙarar horn da sauri Uwani ta sungumi jakar kayanta, ta ɗauko hijabinta ta saka. Sai da ta yi wa mutanen gidan sallama da Aramma sannan ta ƙarasa bakin motar cikin murna, don tun daga nesa ta hango motar baba Mamman. Don haka da saurinta ta buɗe motar tana faɗin. "Daddy wallahi na yi kewar Dada, ƙila ma ita tana can ko a jikin..." Kalamanta suka maƙale a maƙoshi sakamakon ido biyu da suka yi da Jafar. Wata uwar harara ya banka mata, ta yamutsa fuska tana ƙare masa kallo ta ce. "To kai kuma ina motarka ka ɗauko ta Daddy?" Jafar bai tanka mata ba ya fisgi motar da gudun gaske har sai da wasu yara suka matsa a guje. Suna cikin tafiya babu wanda ya tanka wa wani sai Uwani ta fashe da dariya har da ƙyaƙyatawa, a fusace Jafar ya waigo ya zuba mata manyan idonsa. Sai kuwa Uwani ta sake kwashewa da dariya, gangara motar ya yi ya faka ya ɗauke kai gefe a daƙile ya ce. "Fice mini daga mota." Uwani ta gimtse dariyarta sannan ta ce. "Kamar ya na sauka ai ba motarka ba ce." "Uban me kike wa dariya?" Uwani ta yi murmushi ta ce, "Wallahi dariya ka ba ni, ni dai ba baƙuwa ba ce a wurinka atoh. Kuma dai komai na ka Dada ta ba ni labari tun kana jariri har fa tunbiɗin da ka dinga yi kana yaro. Sai kuma na ga ka fafaki mota kana yin wani irin tuƙin 'yan Kaduna-Zaria, to wai ni birgar me za ka yi mini?" Jafar ya haɗiyi wani yawu mai ɗaci haɗe da fusgar da iska mai zafi, jin irin maganganun da Uwani ta faɗa masa. Yana shirin yin magana Uwani ta sake sakin wata dariyar tana faɗin. "Kasan Allah yadda ka iya fafakar motar nan da Inuwan Toyota zai ganka tsaf zai ɗauke ka kwandasta, saboda wataran idan ya gaji ya ba ka ɗani..." "Fice mini a mota." Ya furta mata cikin tsawa. "Wallahi ba zan fita ba ai motar Daddy ce, malam kada ka yi mini gori ni nan gaba ma jirgin sama zan tuƙa." Kalamanta na ƙarshe suka kusa ba shi dariya. 'Yarinyar da cikakkun sentence na hausa ma ba ta iya haɗawa ba ita ce za ta tuƙa jirgin sama.' Ya raya a ransa. Ganin za ta ɓata masa lokaci ya sa ya fisgi motar ya ci gaba da sharara gudu, har suka ƙarasa gida wani bai sake kula kowa ba. Tun Jafar bai gama faka motar ba Uwani ta suri jakar kayanta ta ɓalle murfin motar ta fice a guje ko rufe motar ba ta tsaya yi ba, tun daga soro ta fara ƙwalla wa Dada kira tana washe baki. Mami da ta rako aminiyarta Hajiya Falmata ganin Uwani ya sake tado mata da wani malolon baƙin ciki. "Ƙwata wannan abar ce fa aka aura wa Jafar, imagine a ce wannan ce sirikata." Hajiya Falmata ta ƙare wa Uwani kallo sannan ta saki wani malalacin murmushi ta furta. "Haba ƙawata wai da wannan 'yar abar ce ke barazana da aurenki? Tun da ƙuruciya ba ki yi yaji ba sai yanzu? Babu inda za ki, matuƙar kin bi duk tattaunawar da muka yi wallahi na faɗa miki da ƙafarta za ta kori kanta babu boka babu malam." Sai a lokacin Mami ta ƙara jin ƙwarin gwiwa, Hajiya Falmata ta ci gaba da biya mata miyagun shawarwari sannan suka yi sallama. Da murna Dada ta tarbi Uwani don ita kanta ba ƙaramin kewarta ta yi ba, dalilin da ya sa tun safe ta sa baba Mamman ya ɗauko ta. Shi kuma ya ce a bari zuwa bayan azahar sai Jafar ya ɗauko ta. Kuma ya yi haka ne domin so yake kafin lokacin tariyarsu su ƙara samun fahimtar juna. Sai da aka yi sallar Margriba kamar yadda Baba Yunusa ya ce za a zauna ya tara 'yan uwansa, Dada, na Madina, Uwani, Jafar da kuma Mami. Sai da ya buɗe taron da addu'a bayan kowa ga gama sannan ya fara magana. "Alhamdu Lillah! Na san wasu daga cikinku sun san dalilin wannan zaman yayin da wasu kuma ba su sani ba. Maƙasudin zamanmu a kan kai Jafar da kuma ke Uwani ne." Jafar ya sunkuyar da kai ƙasa rai a bace. Tsabar takaici ya sa Mami yin ƙwafa a fili, Dada ta dube ta haɗe da taɓe fuska ta ce. "Aure dai Allah Ya haɗa duk mai hassada sai rabo ya kashe shi, yara su haihu kuma a mayar da sunansa." Mami ta shiga aika wa Dada harara a fakaice. "Jafar a yanzu wani nauyi ya hau kanka domin aure ba wasa ba ne, ka riƙe yarinyar mutane amana don a yanzu da kake gani komai nata ya dawo ƙarƙashin ikonka. Ke kuma Uwani wannan da kike gani aljannarki na ƙarƙashin ƙafarsa, ki bi mijinki sau da ƙafa yi na yi bari na bari. Duk abin da kika san zai faranta ran mijinki shi za ki yi, abin da ba ya so sai ki haƙura da shi don zaman aure ɗan haƙuri ne." Sai da Baba Yunusa ya numfasa sannan ya ci gaba. "Mun tattauna ni da 'yan uwana a kan za ku tare tare da Mahaifinku tun da an riga an ɗaura aure babu fa'idar a ce za a zauna har sai nan da wata biyu idan auren su Shukra ya zo. A don haka idan Allah Ya kai mu ranar Laraba mai zuwa ne mahaifinku Mamman ya ce za a ƙarasa gyara komai da saka komai na gidan, tun da akwai wadataccen wuri za ku zauna a ƙaramin part ɗin da ke gefen na Maminku." Wani irin tuƙuƙin zafi ne a zuciyar Mami har za ta ƙi amimcewa da hakan sai kuma ta tuna da huɗubar ƙawarta Hajiya Falmata. "Saboda haka muka yanke shawarar idan Allah Ya kai mu juma'a mai zuwa ne tariyarku, kuma bayan nan za a nema wa Uwani wata makarantar za ta ci gaba da karatunta. Idan ya so bayan sun yi hutu sai ka ɗauki matarka ku wuce wurin aiki." Jafar ya yi shiru ba tare da ya amsa ba. Wannan maganar ta ƙarshe ba ƙaramin daɗi ta yi wa Mami ba, don a wannan lokacin ne za ta ci karenta babu babbaka a kan Uwani. "Ni iya abin da zan iya ce wa kenan, Dada kafin mu zo kan ki ko akwai mai magana a cikin?" Gabaɗaya suka girgiza kai ban da Baba Mustafa da ya ce yana da abin cewa. "Sannu da ƙoƙari Yaya Allah Ya ƙara girma, duk bayananka a kan tsari suke. Amma abin da nake gani me zai hana a ɗaga tariyar ta su zuwa nan da kamar sati biyu zuwa uku, duba da yanayin ragowar shirye-shiryen da ya kamata a yi musu. Daga haɗa lefe har zuwa wani shirye-shirye na su na mata, sannan a wannan lokacin mahaifiyar yarinyar na cikin halin rashin 'yarta. Amma bayan wannan lokacin ita kanta za ta samu nutsuwar gudanar da bikin yadda ya kamata." Dada ta jinjina kai sannan ta furta. "Wallahi Mustafa ka yi kyan kai, saboda Allah kamar gajiya na yi da Uwanin da za a ce nan da kwana huɗu a kai ta ɗakin miji." Baba Yunusa ya yi murmushi ya furta. "Wannan haka ne, Dada me za kike ganin ya dace bayan haka." Dada ta yi jim sannan ta furta. "Ni dai kam nasiha ce zan yi wa Jafaru da ita Uwani, amma kam ba yanzu zan yi musu ba sai ranar da za su tare. Don ina gudun na tofar da yawun bakina a banza, su barbaɗar da nasihar da na yi musu tun kafin tariyarsu." Tambayar Mami aka yi ko tana da abin faɗa ta ce babu, don haka suka ƙarƙaren zaman tun ba a gama addu'a ba Mami ta sa ƙafarta ta fice rai a ɓace. 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA GOMA Tun daga wannan ranar su baba Yunusa suka shiga hada-hadar shirye-shiryen tariyar auren Uwani da Jafar, a ɓangaren baba Mamman sai abin ya haɗe masa biyu ga tariyar su Mami ga kuma ta shirin su Jafar. Babba Mamman da kansa ya kira Jafar ya nemi da ya bada wani abin domin ba don da auren ya zo a haka ba, ba shi da tsarin haɗa wa ɗa namiji lefe sai dai ya yi komai da kansa ko ya fi ganin darajar auren da aka ba shi. Amma fir Jafar ya ce ba shi da wasu wadatattun kuɗi, sai da ya ga ran mahaifinsa ya ɓaci sosai sannan ya iya bayar da dubu ɗari uku. Su ma sai da Baba Mamman ya yi masa barazanar zai ɗaga wani filinsa ya sayar a haɗa wa Uwani lefen da shi sannan ya bayar. Mami ban da 'yan uwanta babu wanda ta iya gaya wa sai kuma ƙawarta Hajiya Falmata da ta san da maganar, babban tashin hankalinta kada Hajiya Salima ta ji labari ta ce Safna ba za ta auri Jafar ba. Don haka ta kira Jafar a ɗaki ta gargaɗe shi a kan ko da wasa kada ya sake ya faɗa wa Safna maganar aurensa, don a yadda ta tsara auren ko wata biyu ba zai rufa ba Uwani za ta bar gidan da ƙafarta. Dada da ƙafarta ta je har garinsu mahaifiyar Maryama ta sanar da su duk halin da ake ciki, ba ƙaramin murna suka yi ba suka yi fatan alheri. Haka Dada ta sa aka dinga sanarwa da jama'a wunin bikin Uwani, shi kuwa Jafar har kawo lokacin kallon abin yake kamar a mafarki. Yana shiga ɗakin abokinsa Amir zama ya yi a gefen gado ya zuba uban tagumi, labule Amir ya ɗaga ya shiga hannunsa ɗauke da karan sigari yana zuƙa. Da mamaki ya dubi Jafar ya furta. "Abokina yaushe ka shigo? Kai fa daɗina da kai ka yi wa mutum zuwan bazata, yanzu kuma da ka zuƙi warin 'yar so sai ka hau ni da sababi." Jafar bai ɗago ba ya furta. "Miƙo mini kara ɗaya ka ba ni lighter zan zuƙa." Baki sake Amir ya ƙarasa bakin gadon ya ce. "Ko dai mafarki kake abokina?" "Na ce ka ba ni." Jafar ya faɗa a ɗan zafafe. Ba musu ya miƙa masa, Jafar ya hau kiciniyar kunnawa. Ganin ya kasa saboda rashin sabo ya sa Amir ya karɓa ya kunna masa, Jafar ya kai baki ya zuƙa da ƙarfi lokaci ɗaya ya ƙware ya hau tari. "Malam za ka kashe kanka a banza da wofi, wai me yake faruwa ne?" "Da zan mutu ɗin ma ai da ya fi mini komai sauƙi." Cikin zaro ido Amir ya ce. "Wa ya ɓata maka rai ne?" Jafar ya kauda kai gefe murya a dashe ya ce. "Aure aka yi mini." Amir ya shafa gemu yana sakin wani murmushi sannan ya furta. "Ɗan iskan ƙarya. Kai yanzu don an maka auren ne har kake wannan..." "Ka san wa aka aura mini? Uwani fa, wannan ƙanwar ta wa da ta taɓa sace maka tayar mashin." Jim Amir ya yi da sauri ya ce. "Wai wannan black beautyn? Amma fa kai shege ne, ka tsinci dami a kala ka zauna ka na sa kanka a damuwa?" Kalaman Amir suka ɓa ta ran Jafar bai tanka masa ba ya saka kai ya fice. Kafin ya ƙarasa fita Amir ya ce. "Billahillazi ni zan ɗauki nauyin kazar amarci idan muna raye." Jafar ya dawo da kansa a ƙufule ya ce. "Sai dai ka cinye abarka don ubanka." Amir ya bushe da dariya sannan ya bi bayan Jafar, sai da ya shawo kansa da ƙyar sannan ya labarta masa yadda auren na sa ya kasance. Sam Amir bai ga abin damuwa ba, don ce masa ya yi bayan auren Uwani babu jimawa kawai ya auri Safna tun da ita ce zaɓinsa. Kamar yadda baba Mamman ya tsara juma'ar da ta zo a ita ce su Mami suka tare a sabon gidansu, babban gida ne sosai don haka Mami ta ƙara jin kanta ya daɗa girma. Ta dinga kallon Facalolinta tana basarwa don ita a yadda ta so sam ba ta so sun kwaso jiki da gayyar 'ya'yansu sun zo mata ba. Yamma liƙis suka fara haramar tafiya a nan ne kuma baba Mamman ya ce Dada ba za ta tafi ba sai ta yi kwana biyu. Da yake a part ɗin su Mami har da ɗakin Dada da banɗakinta a ciki, fasalin gidan ba ƙaramin birge Uwani ya yi ba. Don haka da ta ji Dada ta ce ba a ranar za su tafi ba ko a jikinta. Mami ba ƙaramin haushi ta ji ba, don dai tana shakkar Daddy shi ya sa ba ta yi wa Dada kora da hali ba har suka gama kwanakinsu suka koma. Sannu a hankali kwanaki suka fara gangarowa har bikin su Uwani ya ƙaraso, shirye-shirye daga kowanne ɓangare ya yi nisa. Dangin mahaifiyar Uwani da mahaifiyarta ba ƙaramin ƙoƙari suka yi ba, haka su baba Yunusu su suka yi wa Uwanu komai har da su gara. Ƙawayen Uwani su Zulai, Hansatu, Furaira da Kubra sai rawar kai suke su a dole ga manyan ƙawayen amarya. Jafar kuwa ya yi wata irin rama ya ɗan yi duhu kamar shi ne macen, ita kuwa Uwani ko ajikinta sai ma warkajaminta take yi. Ranar juma'a ita ce ranar da aka yi kamun Uwani kuma a ranar ne za a kai ta, tun ranar alhamis aka rangaɗa wa Uwani lallen dungulmi hannu da ƙafa. Ranar Juma'a da sassafe Dada ta ja Uwani uwar ɗaki ta ce. "Uwani ni kam ina kunyar a kai ki ɗaki da wannan uwar kwarkwatar, kin san dai Jafaru da tsirfa tsiya. An ya ba aske miki kan nan zan yi baki alaikum, ba tare da wani ya sani ba." Ita kanta Uwani kan ya ishe ta ga yawa ba gyara ga kuma kwarkwata, don haka ba ta musa wa Dada ba. Da kanta ta karɓi kuɗi ta sayo reza, kamar masu yin wani ɓoyayyan sirri haka Dada da Uwani suka shige uwar ɗaki. Da farko almakashi Dada ta sa ta fara sauke mata kan tass sannan ta bi shi da reza ta yi mata ƙwal kwabo. Nan take Uwani ta ji wata ni'imtacciyar iska na shiga kanta, Dada ta bi ta banɗaki ta wanke mata kan tass sai ga kan Uwani ya fita ƙwal kamar bayan silba yana sheƙi. Bayan Uwani ta gama shiri ta kawo ɗankwali ta ɗaure kanta da shi, tun da ta ji iska na shigarta ta ci alwashin daga ranar idan kanta ya taru aski za ta dinga yi. A daren ranar ne kuma aka shirya Uwani domin kai ta ɗakin mijinta, saboda haka Baba Yunusu ya tara 'yan uwansa aka yi wa Jafar da Uwani nasiha. Uwani na daga cikin mayafinta sai satar kallon iyayen nata take, Jafar kuwa ya haɗe fuska ya sunkuyar da kai ƙasa abin duniya ya haɗe masa. Har an zo fita da Uwani sai Dada ta ja ta gefe ta fara yi mata raɗa a kunne, lokaci ɗaya sai ji aka yi Uwani da Dada sun bushe da dariya. Bayan Dada ta gama mata nasiha sai kuma ta rushe da kuka, sai da aka lallashi Uwani sannan suka wuce Dada ta riƙe hannun Jafar da Uwani suka shiga mota. Ragowar 'yan kai amarya kuma suka bi sauran motoci aka wuce da su gidan Mami. Sai da Dada ta kai Jafar da Uwani har sashen Mami domin ta yi musu nasiha, a yatsine ita da 'yan uwata suka tarbe su don yadda ta hangi Uwani tare da Jafar har ji ta yi kamar ta shaƙe ta. Su Dada na fitowa suka ci karo da su Amir shi da wasu abokan Jafar guda biyu. Dada ta wuce da Uwani sashenta shi kuma ya wuce wurin su Amir. "Ango ango!" Amir ya furta yana dariyar ƙeta. "Kai ba na son iskanci." Jafar ya faɗa a daƙile. "Wato wata miyar fa sai dai a maƙota, abokina ga fa alƙawarina na cika." Amir ya yi maganar cike da shaƙiyanci yana ɗago masa ledar kaji. Jafar duk tsiyar da suke yi masa shiru ya yi ya ƙyale su, ganin dare ya fara yi ne ya sa suka tilasta masa shiga cikin gidan. Har kan gado Dada ta kai Uwani, suna shiga ɗakin Uwani ta fisge mayafin tana kalle-kalle. Dada kuwa sai murmushi take tana sa wa su Baba Yunusa albarka. Sai da Dada ta zo tafiya a nan ne fa Uwani ta maƙele ta tana wani irin kuka mai ban tausayi, ita a dole sai Dada ta zauna. Sai da Inna Atika ta zare wa Uwani ido sannan ta koma laƙwas kan kado ta zauna. Gabaɗaya manya suka tafi daga Uwani sai ƙawayenta su Furaira. "Ke kam Uwani a duniya me za ki nema? Ga miji kin samu ga gidan miji kamar na kwamihina. To ke kuwa kukan me za ki yi?" Furaira ta faɗa, da yake duk cikinsu ta girme musu nesa ba kusa ba. Uwani ta goge ƙwalla nan take su Furaira suka dinga yi wa Uwani huɗuba kala-kala, wani su ƙyalƙyale da dariya wani kuma su tashi su gwada abin da suka ce Uwani ta yi. Suna cikin haka sai ga sallamar su Amir, Uwani da sauri ta ta ja mayafi ta rufe fuska tana murmushi, ita a dole irin kunyar nan ta amare. Tun da su Amir suka shigo Furaira take wata irin kwarkwasa, bayan sun gaisa a gefe ta hangi Jafar ya sunkuyar da kai ƙasa. Furaira ta ƙarasa gabansa fuskarta cike da ɗige-ɗige ta saka mayafin a kafaɗa, ga wasu hannuwan jajayen rigar mama da suka leƙo ta kafaɗarta. Furaira yi farrr da ido ta ce. "Angonmu na ga kana cikin damuwa, idan ka yi haƙuri za mu ba ku wuri kai da amaryarka ku gwangwaje amarcinku, wannan tagumin ai ba naka ba..." Tun da Furaira ta fara magana Jafar ya kafe ta da ido yana kallon tsana, wani irin takaici ya mamaye shi. Jin abin da ta faɗa ya sa ya ɗago ya ɗauke fuskarta da mari. Sai ga Furaira daɓar a ƙasa, waɗansu manyan tagwayen taurari na yi mata yawo a fuska. Ganin abin da ya faru da Furaira ya sa su Zulai suka fita a guje har mayafai da ɗankwalayansu na faɗuwa ƙasa. Amir na shirin magana Uwani ta buɗe kai daga cikin mayafi ta furta. "Haba Ya Jafar yanzu a gaban abokanka za ka zubar mini da mutumci? Furaira fa ka mara gaskiya ba ka..." "Rufe mini ba ki." Jafar ya buga mata tsawa, sai da ta muguɗa masa baki sannan ta shiga wurga masa harara don a wannan karon Jafar ya ba ta haushi sosai. "To ango mu dai maƙasudin zuwanmu shi ne..." Da sauri Jafar ya katse Salis. "Ba na son hayaniya Salis sai da safe." Amir ya gimtse dariya yana miƙa masa ledar kajin hannunsa ya ce. "Au har korar mu kake, shegen gora mum muna kan hanya..." Gabaɗaya sauran abokan Jafar suka saka dariya, sai da suka yi wa Uwani sallama sannan suka fita. Uwani saboda ɓacin ran abin da ya yi wa su Furaira ko tanka musu ba ta yi ba. Jafar na raka su ya koma falo ya zaune, a gajiye ya tuɓe babbar rigar jikinsa ya faɗa kan kujera yana lumshe idanu. Wayarsa ce ta fara neman agaji, da sauri ya ɗago ya duba. Safna ce ke kiransa don haka ya yi rejecting sannan ya kira ta. "Baby wuni guda ka manta da ni." Daga can ɓangaren ta furta a shagwaɓe. "Ta ya ya zan manta da ke cutie?" Ya amsa mata. "Akwai wanda ya taɓa mini gwarzona ga dukkan alamu, baby me yake damunka? Kwana biyu na gagara gane kanka." Murmushi Jafar ya yi sannan ya furta. "Daddy ne ya saka ni wani aikin so na gaji sosai." "Ok, ka yi wanka ka huta da safe ma yi magana becouse akwai maganar da nake son yi da kai." Dam! Ƙirjin Jafar ya buga ba tare da ya san dalili ba, ya yi ƙarfin halin amsa mata sannan suka yi sallama. Tun bayan fitar su Jafar Uwani ta fisge mayafin kanta, ta shiga ɓuruntun duba ɗakin ta buɗe wannan ta leƙa wannan. Bayan ta gama dube-dubenta ta koma bakin gado ta zauna, tuno huɗubar su Furaira ta yi da wacce Dada ta yi mata sai kawai ta saki murmushi. Banɗaki ta faɗa ta yi wanka, sannan ta buɗe akwatin lefenta ta zaro wata doguwar riga. Sai da ta ɗaga wata riga ta ƙare mata kallo sannan ta furta. "Ashe shi ma ya Jafar ƙwallon ɗan iska ne a fakaice ban sani ba, dubi irin rigar fitsararrun indiya da ya sa aka sayo mini. Allah Ya sawaƙe ina zan yi wannan lalacewar Dada ta ga ya wa baba Mamman, haka kawai ya yi mini faɗa." Uwani ta cusa rigar cikin akwatin sannan ta zaro wasu riga da wando ta saka. Sabuwar hula ta farke ta saka a kan ƙwaryar molon kanta, sai kuma ta ciro wasu sababbin panties da rigar mama guda bibbiyu ta farke tana dariya. Can drower kayan Jafar ta buɗe ta jefa guda biyu sai kuma ta taka gado ta saƙale biyu a saman drower, ta koma tana bin ledar kajin da kallo ƙamshi na dukan hancinta. Ganin Jafar ba shi da niyyar dawowa ya sa ta ɗauko ledar kajin da sauran kayan shaye-shaye ta baje ta hau lodawa cikinta. Uwani na nan zaune Jafar ya shiga ko kallon ƙurarta bai yi ba ya nufi drower kayansa domin ya ɗauki towel zai shiga wanka, yana buɗe drower sai jin abu ya yi a kansa rigar mama ta faɗo. Dama Uwani su Furaira sun ce ta yi haka ne, wai yin hakan na jan hankali ango da ƙara danƙon ƙauna. Shi kuwa Jafar yana buɗewa da ya ji abu ya faɗo kansa yaraf da sauri ya buga uban tsalle yana faɗin. "Wayyo ɓera, wayyo Allah ɓera a kaina." Uwani na daga wurin da take zaune sai dariya take, a gefen kafaɗarsa ya hangi rigar a fusace ya fisge a yatsine ya furta. "Mene ne wannan." Uwani ta kanne dariyarta ta ɗan basar ta ce. "Me ka gani to? Ba kai ka saƙalo a jikinka ba? Wai dama duk wannan muzuran da kake yi tsoron ɓera kake?" Jafar ya fisge rigar ya wurga mata, ya ƙarasa ya bige bakinta haɗe da matse shi da hannunsa. "Idan ba ki daina mini rashin kunya ba sai na fasa bakinki." Towel ya ɗauka har zai shiga toilet ɗin da ke cikin ɗakin ko me ya tuna sai ya fice ta nufi public toilet, bayan ya yi wanka ya ɗauko filo ya dawo falo ya kwanta. A kan kujera ya kwanta ya ji kwanciyar babu daɗi ya miƙe kenan ya ji bugun ƙofa, kafin ya tambaya ya ji muryar Mami da sauri ya buɗe Mami ta shiga tana bin ɗakin da wulaƙantaccan kallo. "Ina kucakar nan take?" A sanyaye Jafar ya nuna ɗaki, kamar Uwani ta san da ita take sai ga ta ta leƙo falon hannunta ɗauke da cinyar kaza tana ci. "Ke don Ubanki ba a koya miki ladabin gaida manya ba ne?" Mami ta furta cike da tsana. "Mami na ce miki ki daina zagin iyayena musamman mahaifina da yake lahira..." Jafar ya katse Uwani cikin tsawa. "Ke ba ki da hankali ne? Idan Mami na magana na sake jin bakinki sai na yi ƙasa-ƙasa da ke." "Ka bar ta ba sai ta rama zagin da na mata ba, 'yar iskar yarinya marar mutumci. Ban da ƙaddara ko a mai aikin gidan Jafar za ki zo ne." Uwani ta kafe Mami da kallo, Mami ta mayar da kallonta wurin Jafar. "Kai kuma ka lura da kanka, atoh ka dai gane abin da nake nufi. Wallahi ko da wasa kada na ji ka tsaya sauraron yarinyar nan ballantana wani abu ya ratsa tsakaninku, don wannan tsinannan auren wallahi ko wata biyu ba na saka ran ya kai ba." Jafar ya ɗan tsuke fuska. "Me kike faɗa ne Mami don Allah? Yarinyar da ko kallonta ba na son yi." Zuciyar Mami fes ta ce. "Shi kenan Son Allah Ya yi maka albarka. Ke kuma da ma gobe kina yin sallar asuba ki zo sashena ina son ganinki, shegiyar yarinya da ido kamar na mujiya." Uwani na tsaye ta ji zuciyarta babu daɗi. Wannan shi ne karo na farko da wani ya taɓa yi mata abin da ya bugi zuciyarta, tana nan tsaye ta sake jin muryar Mami a kanta. "Don uwarki ba magana nake yi miki, 'yar iska yarinya tsohuwar kakarki ta sangarta ki kina iskanci kala-kala. Da ƙafarki sai kin bar gidan nan da ni kuke zancen." Uwani ta sauke ajiyar zuciya rai a ɓace ta furta. "Mami wannan ce magana ta ƙarshe da zan gaya miki a kan zagin iyayena, zan jure komai amma ban da zaginsu. Dada ta daban ce a wurina amma matuƙar kika ci gaba da zaginsu ni ma..." Maganar Uwani ta katse sakamakon marin da Jafar ya sauke mata. Take idonta ya ciko da ƙwalla ta dube shi za ta yi magana ya katse ta. "Uwata ba sa'arki ba ce..." "Kenan ni iyayena ne sa'anninta? Wallahi ba zan jura ba..." Tas tass Mami ta sake ɗauke fuskar Uwani da mari. "Na zagi Uwarki sai ki rama don ubanki." Ban da ruwan hawaye babu abin da Uwani take yi, Mami ta gama ci mata mutumci sannan ta fice daga ɗakin. Tsaki Jafar ya saki ya wuce ya ɗauko bargo ya koma falo ya shimfiɗa ya kwanta zuciyarsa na suya, ta koma ta ɗauko mayafinta ta yafa ta zo za ta fice. Da sauri Jafar ya fisgo ta fuska a haɗe ya ce. "Gidan uban wa za ki a tsohon daren nan?" "Gidan da na fito tun da nan ba gidan zinare ba ne." Uwani ta ba shi amsa a zafafe. Tana gama magana ta sake miƙewa za ta fita ya sha gabanta. "Wallahi ba don Daddy na gidan nan ba, da babu abin da zai sa na hana ki fita. Shashasha ƙazamar banza da wofi." Daga haka Jafar ya sa key ya rufe ƙofar. Uwani ta koma ciki rai a ɓace. A ƙasa ta zauna tana nazarin hanyar da za ta samarwa kanta mafita, don ta tabbata idan ta ce a haka za ta ci gaba da zama a gidan nan ba za ta sha ruwa ba. Kuma ita dai wannan ƙerarran gidan ba za ta so ta fita daga shi ba ko don ta dinga cin daɗi kuma ta gyara wa Mami zama. Ƙurajen da suka fara tsattsafo mata a kai ne suka fara yi mata raɗaɗi, don haka ta ɗauko jakarta ta ciro farar hoda ta bursune kanta, fuskarta har zuwa wuyanta. Hamma ta fara saki tana gyangyaɗi ba shiri ta ɗauki fulo ita ma ta nufi falo. A lokacin da ta shiga falon Jafar har ya kashe fitilar falon ya yi bacci, a gefe ta yarda filonta ta kwanta ita ma nan take bacci ya yi awon gaba da ita. Lokacin da dare ya tsala Jafar na cikin bacci juyin da zai yi sai jin mutum ya yi a kusa da shi, a tunaninsa Uwani ce don haka ya miƙa hannu sai ji ya yi ya shafo kan mutum da rantal da aski. A zabure ya tashi yana faɗin. "Kwarto ne zai shigo mana gida." Ya ɗaga hannu da ƙarfin gaske ya ɗaka wa Uwani duka a baya a tunaninsa kwarto ne. Tun da ya san ban da haka babu abin da zai kawo namiji ya kwanta a kusa da shi. A zabure Uwani ta tashi tana susar baya, sai a lokacin Jafar ya kunna fitilar ɗakin. Cikin tashin hankali ya fara ja da baya ganin baƙuwar fuskar da ya gani fururu da hoda, a hankali Uwani ta fara tunkaro shi. Jafar ya fara ja baya yana faɗin. "Don Allah waye kai?" Uwani ta ci gaba da matsowa ganin ta tunkaro shi gadan-gadan ya sa Jafar ya zuba a guje ya fice daga ɗakin yana faɗin. "Wayyo Allahna." Ita ma Uwani ta rufa wa Jafar baya a guje tana gudu tana wani irin gurnani. Daga yau zan tafi hutun sallah sai ranar Laraba (19/06/2024) zan ci gaba da posting In Shaa Allah. Littafin Uwani 500 ne amma daga yau zuwa ranar Laraba 19/06/2024 duk wacce ta za biya za ta turo 400 ta wannan Acc ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank Evidance ta wannan number 07062062624 na rage muku 100 for Happy Sallah. Idan kuma littafi ya zama Complete 800 ne, mutanen Nijar su tuntuɓe ni. Ina fatan 'yan uwa za a bi nama saffa-saffa don gujewa rikicewar ciki.😂 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA SHA ƊAYA Ilahirin jikin Jafar ban da karkarwa babu abin da yake yi, iya ƙarfinsa ya taƙarƙare yana gudu tun don tun da ya zo duniya bai taɓa cin karo da hallitar da ta ba shi tsoro lokaci ɗaya kamarta ba. Tashin hankalinsa ya ninku sakamakon jin ƙofar da za ta sada shi da gareji ta datse ƙam ta ƙi buɗuwa, ganin haka ya sa Jafar ya maƙale wani dogon ƙarfen da ke jikin rumfar harabar wurin. Cangala ƙafa Uwani ta fara yi ta fara wata shaƙuwa da ƙarfi tana zaro ido waje ta tunkare shi. Hannu ta sa ta fisgo ƙafarsa ɗaya sannan ta ce. "Sai mun fige wannan ƙafar taka kamar yadda ake figar kaji, sannan mu ɗauke ka mu tafi da kai dajin tsumbur. Tun da har muka buɗe maka idanu kana iya ganin mu sai mun tafi da kai." Jafar a ruɗe ya furta. "Wayyo Mami, wai Daddy ba kwa ji na ne? Ku taimaka mini kada su fige ni." Uwani ta fara wani juya idanu tana buɗe baki kamar mai shirin kai cizo, sai da ta sake zaro ido waje sannan ta kai baki ta gasa wa Jafar cizo a ƙafa. Ta sa hannunta na hagu ta yaƙuso ƙwaurinsa, ta ci gaba ta fisgar ƙafar tana faɗin. "Ɗan tsita yau balangu za ka ci, sai mun babbake maka wannan cinyar guda ɗaya mai kama da ta sauro ka cinye." Cikin azaba ya fisge a nan Allah Ya ba shi nasara ya buɗe ƙofar, ganin ɗakin Lado mai gadi ya fi kusa da shi ya sa ya nufi wurin a guje yana tafe yana waige. Abin da ya ƙara ɗaga masa hankali, bai wuce yadda idan ya waiga yake ganin Uwani na sake tunkaro shi tana zaro harshe waje. A wannan karon Uwani ta sauya salon tafiya a hankali take tafiya tana zaro harshe, ta sake karkatar da kai ƙasa kamar yadda zombie suke yi. Lado mai gadi da ke zaune a kan kujera cikin gyagyaɗi ya ji gudun Jafar, a zabure ya miƙe yana faɗin. "Ranka shi daɗe lafiya kuwa?" Jafar ko ta kan Lado bai bi ba ya banke shi ya faɗa ɗakinsa ji kake garam! Ya doko ƙofar ya rufe, dabass! Lado ya faɗi saboda bangazar da Jafar ya yi masa ya yunƙura yana kaɗe jikinsa ya furta. "Allah na tuba wane dare ne jemage bai gani ba? Ai sai daren mutuwarsa. Ni akwai wani aljani ko ɗan fashi da zai razana ni, ni da tun ban fi shekara biyar a duniya ba Baffa ya fara kwana da ni a wurin gadi..." Maganar Lado ta maƙale sakamakon hango Uwani da ya yi tana tafe tana ƙaƙƙanbare hannu, 'yar ƙaramar sandarsa ya ɗauka zai tunkari Uwani tsoro ya fara kama shi. Lado ya fara waige hankali a tashe ya cewa Jafar. "Yallaɓai! Wai mene ne ma ya karo ka daga cikin gidan ne." Muryar Jafar a can ƙuryar ɗaki ya ce. "Lado gamo na yi don Allah ka yi wani abu a kai." Lado ya fara tunkarar Uwani gabansa na faɗuwa, sai da ya tafi gadan-gadan kamar zai iya taɓuka wani abu sai kawai ya zuba a guje ya fara doka ƙofar ɗakinsa. Jafar na jin an fara doka ƙofar ɗakin Lado wani abu ya sake tsarga masa, jiki na karkarwa ya ce. "Lado ya ake ciki ne kar dai sun fi ƙarfinka kai ma?" Lado da ke cikin tashin hankali ganin Uwani ta zo daf da shi ya fara fitsare wandonsa ba tare da ya sani ba. Uwani ta fisgi sandar hannunsa tana wage baki, ta zuba masa tana caccaka masa tsinin sandar a baya. Cikin tashin hankali Lado ya fashe da kuka ya furta. "Yallaɓai don Allah ka taimaka mini, ni ma fa na shiga hannu." Jafar da ke cikin ɗakin jin Lado na kuka shi ma sai ya fashe da kuka don ya san tun da aka fi ƙarfin Lado shi ma yana nan ɗakin za su zo su cim masa. Daga can saman window Uwani ta hango Mami na ziro kai tana leƙen abin da yake faruwa, Uwani ta ɗaga kai tana wani gwale fuska ta nuno Mami da sandar hannunta ta ce. "Keeee me leƙen nan! Wallahi za mu mayar da fuskarki ƙeya, mu ɗebo ƙafafunki mu dawo da su ƙirjinki. Shi kuma ƙirjinki mu mayar da shi gadon bayanki." Tun Mami ba ta gama jin abin da Uwani ke faɗa ba ta yi saurin banke gilas ɗin window. Lado na ganin ya ɗan samu sarari ya zuba uban ihu ya nufi sashen su Mami a guje. Uwani ta rufa masa baya tana tafe tana ranƙwala masa sanda a baya, Lado ban da ihu babu abin da yake saki. Jafar da ke cikin ɗakin Lado ya yi sharkaɓa da gumi jikinsa ban da karkarwa babu abin da yake yi. Lokaci ɗaya ya ji zazzaɓi ya rufe masa jiki, a lokacin da ya ji Uwani ta bi Lado a guje da sauri Jafar ya ja zani ya tura kansa a ciki yana kalmar shahada. Lado na tura ƙofar sashen Mami ya tura ƙofar da datse da sakata jiki na rawa, da ƙarfi Uwani ta fara kartar ƙofar tana faɗin. "Za mu jijjige ƙauren gidan mu shigo, mu banka wa mutanen cikin gidan wuta. Ko kuma mu burtso ta ƙarƙashin ƙasa mu kwashe ku tass." A guje Lado ya shiga cikin gidan, da ɗakin Mami ya fara cin karo don haka ya banka da ƙarfin gaske ya faɗa ciki. Mami na kwance a kan gado cikin bargo ban da karkarwa babu abin da jikinta take yi, jin an yi sufa a kan gadon da take ciki an shige bargo ya sa ta yi tsammanin ko Daddy ne shi ma aka tsora ta yake neman ɗauki. Sai da Uwani ta tabbatar da Lado ya gama tsurewa sannan ta yarda sandar ta nufi sashenta, kayan jikinta cire ta saka wata doguwar riga har ƙasa sannan ta shiga banɗaki ya wanke fuskarta ta haye gado ta kwanta abin ta. Duk budurin da ake yi Daddy da su Shukra sam ba su sani ba, da yake Daddy ya tsaya nafilfulu bai kwanta da wuri ba. Kwanciyarsa babu jimawa bacci mai nauyi ya yi awon gaba da shi, da ma Mami ba ɗaki ɗaya suke kwana ba tun ranar da ya je mata da maganar auren Jafar ta yi masa yaji take kwana a ɗakinta. Don haka ko da suka tare a sabon gidan ma, ba ta sauya zani ba. Daga Mami har Lado babu wanda ya gane wanda yake kusa da shi, don haka sai da asuba ta yi Lado ya zuro kai a hankali. A daidai lokacin Mami ta ɗago kai karaf suka haɗa ido da shi, a zabure Mami ta ja da baya fuska a murtuke ta ce. "Lado! Uban me ya kawo ka ɗakina?" Sai a lokacin Lado yake bin ɗakin da kallo, don shi dai bai san lokacin da ya shiga ba. Hankali a tashe ya furta. "Hajiya wallahi sai dai idan kawo ni aka yi! Wallahi ba ni na kawo kaina ba. Aljanun da suka biyo Jafar ne suka kawo ni..." A zafafe Mami ta katse shi. "Fita don Ubanka Lado." Kamar sabon munafiki haka Lado ya fita yana waige-waige, kallo ɗaya za ka yi masa ka fahimci yana cikin tashin hankali. Banɗaki Mami ta faɗa ta ɗauro alwala ta yi sallar asuba, da yake gari ya yi haske sosai fita ta yi ta nufi sashen Uwani. A lokacin da ta fara buga ƙofa Uwani tana kwance, ta fara magana. "Waye?" "Uwarki ce." Mami ta amsa a taƙaice. Babu musu Uwani ta buɗe ƙofar ta furta. "Ina kwana..." "Riƙe gaisuwarki, ina Jafar yake?" Uwani ta wara hannuwa ta ce. "Ni ma ban wayi gari na gan shi ba, yanzu nake shirin zuwa na tambaye ki." Rass gaban Mami ya faɗi, da sauri ta fice daga sashen Uwani ta nufi wurin Lado da ke zaune a kujera yana jin rediyo. "Lado ba ka ga fitar Jafar ba?" Mami ta tambaya. "Hajiya ai Jafar na cikin ɗakina tun daren jiya, yanzu haka na yi-na yi ya buɗe wallahi ya ƙi, ni tsorona ma kada mutanen ɓoyen nan su dawo su tarfa ni a wurin nan." Lado ya ƙarasa maganar wasu tagwayen ƙwalla na zuba. Mami ba ta ƙarasa jin maganar Lado ba ta nufi ɗakin tana bugawa. "Son buɗe mini ƙofa Maminka ce." Daga cikin ɗakin muryar Jafar can ƙasa ya furta. "Mami ku miƙo mini ruwan alwala, ba zan iya fitowa ba wallahi gwagwiye mini ƙafa za su yi." Duk yadda Mami ta so Jafar ya buɗe ƙofar fir ya ƙi buɗewa, Lado ya miƙa masa ruwa ta window da sauri Mami ta nufi sashensu kai tsaye ta wuce ɗakin Daddy. Da sallama Mami ta shiga, turus ta yi ganin Daddy na zaune a kan dadduma yana karatun Alƙur'ani. Ganin Daddy ba shi da niyyar sallame karatun ya sa Mami ta furta. "Daddy gidan nan fa babu lafiya. Domin ganin idona na ga aljanu a daren jiya, yanzu haka Jafar yana ɗakin Lado tun daren jiya ya ƙi fitowa. Ka ga dai yau kwananmu ashirin da biyu a gidan nan ko kunama ba ta taɓa tsoratar da mu ba, amma zuwan yarinyar nan ga shi aljanunta suna neman sabauta mini yaro." Daddy ya kafe Mami da kallo, a daƙile ya furta. "Allah Ya sawaƙe." Ran Mami a ɓace ta ce. "Iya abin da za ka iya faɗa kenan Daddyn yara? An ya kana ƙaunata ni da 'ya'yana yanzu kuwa?" Sai Mami ta fara zubar da ƙwalla. Daddy bai tanka mata ba ya rufe Kur'anin sannan ya naɗe dadduma ya fice daga ɗakin. Duk abin da yake faruwa Lado ya zayyana wa Daddy, Daddy ya isa bakin window ɗakin Lado ya leƙa. Ban da gumi babu abin da Jafar yake yi, da ƙyar Daddy ya shawo kan Jafar ya buɗe ƙofar. Lokaci ɗaya Jafar duk ya yi zuru-zuru, Mami ta ƙarasa ta ruƙo hannunsa tana faɗin. "Son amma babu abin da yake damunka ko?" Uwani da ta ƙarasa ta nuna kamar ba ta san abin da yake faruwa ba ta ce. "Ya Jafar ina ka shiga da asuba na ga ba ka nan." Jafar ya bi Uwani da shanyayyun idanunsa da kallo, Mami ta wurga mata harara sannan ta ja hannunsa suka wuce sashenta. Uwani ta gimtse dariyarta ganin yadda Jafar yake tafe yana ɗimgisa ƙafa, sai ƙara wani shagwaɓe wa Mami yake. Daddy ne ya koma wurin Lado ya sake tambayarsa tsakaninsa da Allah a kan abin da ya faɗa masa, don shi bai yarda da abin da Mami ta faɗa ba. Gani yake kamar wani sabon shirin suka ɓullo da shi, sai da ya ji ta bakin Lado ya kuma nuna masa shatin bayansa wurin da Uwani ta caccaka masa sandar wurinsa sannan Daddy ya yarda. Shiru Daddy ya yi yana nazari, a iya zamansu dai a gidan ba su ga wani baƙon abu ba. Sai tunaninsa ya tsaya a kan ko Uwani tana da iska, ya fi aminta da wannan tunanin na shi a kan mutanen jikin Uwani ne suke yunƙurin tashi tun da dama wasu sai an yi aure suke nuna kansu. Jafar wanka ya yi Mami ta dafa masa tea ya sha sannan ya samu ya kwanta bacci ya yi awon gaba da shi, ita kuwa Uwani tana can zaune Daddy ya leƙa ya kira ta ya ce ta nufi sashen su Mami ta zaune akwai baƙin da zai kira za su yi saukar Alƙur'ani a cikin gidan. A rakaɓe Uwani ta zauna a falon, sai uwar harara da Mami take auna mata don ma Daddy yana gidan amma ta ci burin tun a ranar ta fara hora ta da aikin wahala. Sai kusan sha biyun rana ragowar 'yan uwan mahaifiyar Uwani da wasu tsirarun 'yan uwan Dada suka sake dawowa ganin gidan Uwani, sai a lokacin ne Uwani ta ɗan saki jiki suka dinga hira. Mami ba don ta so ba ta sa Inna mai aiki ta girka musu abinci, bayan sallar la'asar kuma kowa ya kama gabansa. Daren ranar da ƙyar Daddy ya shawo kan Jafar suka koma sashensu, don ita Uwani fir nunaawa ta yi ba ta gane abin da Jafar da su Mami suke faɗa ba. Dalilin haka ya sa Daddy ya sake tabbatar da ƙila mutanen jikin Uwani ne suka tsora ta su. Sai da suka ci abinci a ɓangaren su Mami sannan suka nufi na su, suna zaune a falo zaman kurame wayar Jafar ta fara ringing. Number Safna ya gani bai san dalili ba haka kawai ya ji gabansa ya faɗi, a hankali ya ɗauki wayar daga can ɓangaren aka furta. "Haba Baby wai ina ka shiga ɗazu na kira no respond." Jafar ya saki murmushi. "Cutie na gaya miki kwana biyu ba na zama but am very sorry, In shaa Allah haka ba za ta ƙara faruwa ba." "Beb dama fa Daddy ne na ji yana yunƙurin haɗa ni da wani cousin ɗina, ni kuma na ce masa ina da wanda nake so. So yanzu dai ya ce kawai ka fito..." Tun Safna ba ta gama magana ba Jafar ya miƙe a zabure, "Da gaske kike Cutie?" Jin yadda ya karɓi maganar ne ya sa Safna ta ce. "Da wani abu ne Baby?" Jafar ya ɗan wayance yana sosa ƙeya ya furta. "Am ba komai Dear kawai na yi mamaki ne, na ɗauka Dad ba zai bari a yi maganar aurenmu yanzu ba." Cikin jin daɗi Safna ta ce. "No ka san Daddy bai da matsala." Jafar ya ma manta Uwani na wurin shi da Safna suka ci gaba da hirar soyayya, ya tabbatar mata da zai sanar da mahaifinsa duk abin da ake ciki. Baki sake Uwani ke bin sa da kallo tana mamakin yadda yake sakin murmushi. "Ya Jafar dama kana dariya haka?" Uwani ta tambaya. "Sai ki hana ni, da waya ce ki zauna ki saka mini ido?" Uwani ta tura baki gaba. Suna nan zaune sai ga kiran Dada ya shigo wayarsa. Sai da ta kusa katsewa sannan ya ɗauka yana faɗin. "Tsohuwa mai ran ƙarfe." Dada ta saki murmushi ta furta. "Lallai Jafaru dare guda wai amarci ya ɓoye ka, ja'irin yaro da ana baka ka na ƙin karɓa..." "Kin san Allah Dada zan kashe wayata." Jafar ya furta a taƙaice. "Yoo kashe mana Jafaru, ai ubanka Mamman na nan. Ni ba zan aiki uwarka Saro ba saboda ba ganin mutumcina take ba. Amma wallahi ka kashe mini waya ban gaisa da Uwani ba sai na kira ubanka Mamman ya kawo mata waya." Jafar bai tanka ba ya miƙa wa Uwani waya. "Dada ni dai gaskiya wurinki zan dawo, gidan nan babu daɗi ko kaɗan." Dada ta washe baki ta furta. "Haba Uwanita ai dama gidan aure kowa a sannu yake sabawa, lokacin da aka kawo Saratu uwar Jafaru ta haura wata biyu tana guduwa gida. Amma ba ga shi yanzu Saro ta murje tana zuba mulki ba, ke dai duk shawarwarin da na baki na riƙe miji ki riƙe su gam, kin san dai halin Jafaru da baƙin halin tsiya. Kar dai ki ɓata masa ya sa bakin bindiga ya harbe mini ke." Gaban Uwani ya faɗi, da sauri ta ce. "Kuma sai ya harbe ni fa ko Dada?" Jafar da ke jin duk abin da suke faɗa ya kalli Uwani ganin lokaci ɗaya ta firgice. "Wallahi indai halin Jafaru da na sani ne tsaf zai harbe ki, yo ba Mamman ne ya haifo shi ba. Ai Allah kaɗai ya san haƙurin da Saro take yi da shi, ni ina zargin duk rashin mutumcin da take yi ma Mamman ne ya koya mata. Atoh kowa dai ya san mata na da alkunya, kuma idan kika ga mace ta canza daga mijinta ne. Ni dai yanzu duk wannan hirar da muke yi kada ki bari Jafaru ya ji, don sai ya sanar da Mamman. Ina zaman-zamana tun daga ƙuruciya ban taɓa sanin wurin Hukuma ba Mamman ya yi ƙarata. " Uwani ta ce. "Dada wai ina na Madina ko cigiyata ba ya yi ne? Ina su Lawan kina dai kula da su ko?" Lokaci ɗaya Dada ta bushe da dariya sannan ta ce. "Na Madina fa ya tafi wurin wata Goggon su Sabi'u, ni ban san na Madina neman aure yake ba sai jiya, ashe shi ya sa kullin a cikin sayen turaren binta sudan yake. Ni dama na jima ina yi wa na Madina addu'ar Allah Ya damƙa shi hannu mata ta gari..." "Dada zan yi amfani da wata na gaji da wannan hirar ta ku." Jafar Ya faɗa yana ƙoƙarin karɓar wayarsa. Daga can ɓangaren Dada ta ce. "Jafaruruna gaskiya na ji daɗin yadda na ji zamanku kai da Uwani, amma don Allah ka sayo mata waya ma dinga gaisawa idan kana gida." Jafar zai yi magana Dada ta katse shi. "Kai gaskiya kar ma ka saya wa Uwani waya ka yi asarar kuɗinka, haka kawai kuna zaune lafiya ta haɗa lamba ta kira maka mutanen duniya. Kwanki da ta ɗauki wayata sai ji na yi ta kira wani ɗan yuniyon..." "Shi kenan sai da safe Dada." Jafar ya katse ta yana karɓar wayar daga hannun Uwani. Dada ta saki murmushi ta ce. "Allah mai iko wai Jafaru ne yau yake zumuɗin kashe waya saboda ga mace a gefensa." Ɓacin ran kalaman Dada ya sa ya katse wayar ba tare da ya tanka mata ba. Dare ne ya fara yi don haka Uwani ta gaji da kallon da take yi, ɗaki ta shiga ta fara duba akwati domin ta ɗauko rigar bacci ta saka. Tsulum ta ga Jafar ya shigo da sauri sai wani wuri-wuri yake yi. "Malam ka fita zan sauya kaya." Uwani ta furta. Banza ya yi mata don a yadda ta lura da Jafar kamar a tsorace yake, don haka ta ɗauki wata doguwar riga ta shige banɗaki. Sai da ta sauya kayan sannan ta koma ɗakin, tana shirin hawa kan gado ta ga ya jefa mata filo ƙasa. "Ina zaki je?" "Kwanciya zan yi." Ta amsa masa a taƙaice. "Daga yau a nan ƙasa za ki dinga kwana idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci." Jafar ya yi maganar yana ɗaukan jallabiyarsa ya shiga banɗaki, sai da ya sauya kaya ya fito sannan ya haye gado ya kwanta. Uwani ta ɗauki filon ta koma can gefen gado tana shirin ajiye filo Jafar ya riƙo kunnenta da ƙarfi ya murɗe. "Kin raina abin da na faɗa miki ne? To ki kwanta Allah Ya ba ki sa'a." Ya ƙarasa maganar yana murɗe mata kunne har sai da Uwani ta ɗan ƙwalla ƙara. Babu yadda ta iya haka ta koma ƙasa ta yarda fulo ta kwanta, bayan wani lokaci gabaɗaya bacci ya yi awon gaba da su. Cikin dare Uwani ta ji sanyi ya dame ta ga bargon na su Jafar ya ɗauka ya rufa da shi, cikin sanɗa ta ɗauki filo ta koma can gefen gado ta janyo bargon ta rufa. A wannan karon ma Jafar yana juyowa cikin bacci ya ji ya sake shafo ƙwaryar molo, Uwani da ke bacci jin ana shafa ƙwaryar molon kanta ya sa ta buɗe ido. Da yake ƙeyarta ce ke kallon fuskar Jafar sai ta maƙe murya ta ce. "Kada ka motsa, idan ka yi yunƙurin guduwa sai na tsinke ƙafafuwanka." Jafar na jin haka sai kawai ya taƙarƙare ya rushe da kuka, ya fara biya duk wata addu'a da ke bakinsa. Sun ɗan jima a haka suka ji an fara kiran assalatu, Uwani ta fara wani gurnani tana wani bubbuga hannuwa sannan ta ce. "A yanzu za ka iya fita ka je ka yi sallah." Tun ba ta rufe baki ba Jafar ya buga tsalle ya fice a guje, yana fita ya ci karo da Daddy jikinsa na rawa ya furta. "Daddy wallahi gidan nan da aljanu Allah ba zan ƙara kwana a ciki ba." Ganin yadda jikin Jafar ke rawa ya sa Daddy ya riƙe shi gam a jikinsa, riƙe hannunsa ya yi suka fara tunkarar sashensu. Da sauri Jafar ya fara kiciniyar fisge hannunsa ya ce. "Daddy ina za mu shiga?" Daddy ya saki murmushi irin na manya ya ce. "Trust me son, ka san dai ba zan cutar da kai ba." Shiru Jafar ya yi suna tafe gabansa na faɗuwa har suka shiga, cikin shammata Uwani ba ta yi tsammani ba suka yi ido huɗu da Daddy. Cikin tashin hankali Uwani ta zaro ido, ta kai hannu ta dafe kanta. Na ce kin turo kuɗin littafinki kuwa? Yau promo ɗin zai ƙare💃🏻 faka-faka ki turo 400 Aisha Adam First bank shedar biya ta wannan lambar 07062062624 idan yau ta wuce za ki turo 500 maza hanzarta kada a yi babu ke🫠 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA SHA BIYU Ganin yadda Uwani ta tsorata ya sa Daddy ɗan kawar da kansa, duk da a falo suka ci karo da ita za ta fito. A fili Uwani ta sauke ajiyar zuciya, ta sauke hannunta daga kanta don kaɗan ya rage asirinta bai tonu ba. Saboda ta ɗaura ɗan kwalinta a kanta kenan su Daddy suka shiga. "Barka da asuba Daddy." Uwani ta furta. "Barka dai Uwani me yake faruwa ne?" Daddy ya tambaye ta yana kallon yanayinta. Sai da ta saci kallon Jafar sannan ta ce. "Wallahi Daddy ban sani ba, ina cikin banɗaki na ji ihun Ya Jafar, fitowar da na yi kenan zan bi shi na ga abin da yake faruwa." Ganin yadda Uwani ta rattabo bayani kamar ba ta san abin da yake faruwa ba ya sa Daddy ya aminta da ita, don haka ya furta. "Ki ɗauko hijabinki ki taho sashen Maminku." Daga haka Daddy ya juya, Jafar ya yi saurin bin bayansa. "Ka sako kayanka mana Jafar." Daddy ya katse shi. Sai a lokacin Jafar ya lura daga shi sai singlet da gajeren wando. "Uwani miƙo mini kayana." Uwani ta wuce ɗakin tana ƙumshe dariyarta ganin yadda Jafar ya tsure lokaci ɗaya. Tana miƙa masa kayan ya yi sauri ya sa, yana cikin saka riga Uwani ta janyo hijabinta za ta fita da sauri Jafar ya fisgo hannunta ya ce. "Ina za ki tafi ki bar ni, ki jira ni mana na gama shiryawa. "A wannan karon sai da dariya ta ƙwacewa Uwani ta ce. "Wai don Allah a wurin training ba a fitar da masu tsoro da marasa tsoro ne a cikin aikinku ne?" Jafar ya wurga mata harara. Sai bayan da suka yi breakfast sannan Daddy ya kira Jafar, Uwani da Mami sannan ya fara magana. "Dalilin da ya sa na tara ku bisa wata matsala da ke faruwa daga jiya zuwa yau, a baya ban yi niyyar sanar da 'yan uwana ba amma yanzu..." "Daddyn yara babu fa buƙatar a tsaya ɓata lokaci, raba wannan auren shi ne mafi amfani a gare mu. Ina ji ina gani sheɗanu ba za su kashe mini ɗa ba, wannan yarinyar ba alkairi ba ce a wurinmu face annoba." Shiru Dadday ya yi yana sauraron Mami har ta gama. Sannan ya ɗora da cewa. "Ka buɗe kunenka da kyau ka saurari abin da zan sanar da kai Jafar." Daddy ya furta rai a ɓace. Jafar ya gyaɗa masa kai, Daddy ya ci gaba. "Ga Uwani nan ni da 'yan uwana da kuma mahaifiyarmu mun damƙa maka ita amana, wallahi ko bayan raina idan ka rabu da ita ban yafe maka ba." A hargitse Jafar ya ɗago, Mami na jin haka sai kawai ta rushe da kuka ta fice daga falon. "Dama Daddy cewa na yi zan koma Lagos, saboda gidan nan ba ni da nutsuwa da shi." Jafar ya yi magana yana satar kallon mahaifinsa. Daddy ya jinjina kai ya ce. "Hakan ma ya yi idan kana ganin ya fi a wurinka, amma ka sani a waɗannan kwanakin naka duk inda za ka saka ƙafa sai dai ka tafi da Uwani. Ba zai yiwu kwana biyu da yin aure ka tsallake yarinya ka bar ta a nan ba, sannan kuma wannan matsalar da ke faruwa zan nemar muku magani idan daga kai ne ko kuma daga ita ne." Wani malolon ɓacin rai ya tokare Jafar, ya haɗiyi yawu mai ɗaci ya furta. "Shi kenan Daddy." Daga haka Daddy ya sake yi musu nasiha sannan ya sallame su. Jafar na fita ya kira Amir a waya bayan sun gaisa yake ce masa ga shi nan zuwa, a lokacin da ya je Amir na zaune da Laptop a gabansa yana aikin tracking. Kamar mai ciwon haƙori haka Jafar ya yi sallama ciki-ciki ya zauna a bakin katifa. "Ango ka sha mai, kai ka ga yadda saman hancinka yake ƙyalli. Shegen kaya kana so kana kai wa kasuwa." Amir ya yi maganar yana dariyar shaƙiyanci. "Ba na son iskanci ni ba wannan ne ya kawo ni ba." Jafar ya furta rai a ɓace. Da ido Amir ya bi shi da kallo Jafar ya ci gaba da cewa. "Zuwa na yi ka ba ni aron ɗaki na kamar sati biyu." "Ni kuma na je ina? Ka san dai ai hutu muka dawo ko?" Jafar ya dage kai da hannuwa biyu cikin damuwa, Amir ya sanarwa yadda suka yi da Daddy sannan ya ɗora da cewa. "Allah Ya sani ba zan iya tafiya Lagos da Uwani ba, haba kawai sai na fara nuna ta na ce ga matata. Kuma ka san duk yadda zan ɓoye wa Safna na yi aure matuƙar na je da Uwani sai asirina ya tonu." Jafar ya sauke ajiyar zuciya ransa na ɗaci ya ci gaba da magana. "Ga Safna na shirin ɓallo mini ruwa ita ma." Nan ya kwashe hirar da suka yi da Safna, ya ɗora da cewa. "Abokina don Allah ka ba ni mafita komai ya cushe mini, al'amura duka sun kwaɓe mini." Shiru Amir ya yi yana nazari, da sauri ya ɗago ya ce. "Na samu mafita. Yanzu dai da farko ka ɗauki Uwani ka kama muku hotel, ba ka ce makaranta za a saka ta ba. Idan kuka cinye wannan hutun ka ga ai sai dai ka dinga zuwa ka na dawowa, ita kuma Safna idan har ba jagwal kake son haɗa wa kanka ba to ka yi mata dabara har zuwa nan da bayan kwana biyu, idan ya so kafin nan matsalar Uwani ta ragu sai ka ji da waccan matsalar." Jim Jafar ya yi jiki a sanyaye ya ce. "Sai kuma kawai na koma rayuwar hotel kamar wani ɗan iska." "Wa ya ce maka 'yan iska ne kaɗai ke rayuwar hotel? Masaukin baƙi ne fa. Kuma idan ma iskancin za ka yi ai matarka ka ɗauka ko?" Amir ya yi maganar cikin zolaya. Sun ɗan taɓa hira sannan Jafar ya yi masa sallama ya wuce gida. Daren wannan ranar a ɓangaren Mami suka kwana, Daddy ya sa aka buɗe musu ɗakin Dada suka shiga ciki. Fes yake babu ƙura a ciki, wannan karon Jafar bai kori Uwani daga kan gadon ba saboda a matuƙar tsorace yake. Kowannensu ya juya bayansa ya kwanta, bini-bini Uwani idan za ta gyara kwanciya sai ta ƙara tamke kai da ɗan kwali. Kimanin ƙarfe tara na safe Uwani da Jafar suka shirya kowannensa ɗauke da jaka, Uwani kayanta ta ɗiba ta saka a akwati kamar yadda ya gaya mata. Mami da ta je yi wa Jafar sallama sai jaddada masa take ya kula da kansa tamkar wani mace, shi maganar tata har kunya ma take ba shi. Daddy ne ya ɗauke su a mota ya nufi tashar sabon gari da su, Jafar yana gani bai faɗa masa cewar ya fasa zuwa Lagos ba don nauyi yake ji ya ce masa hotel zai kama musu. Sai da ya tabbatar da motar Daddy ta yi nisa da tasha ya dubi Uwani ya ce. "Sai ki ɗauko jakarki." Ba musu Uwani ta fara jan jaka har suka samu mai adaidaita sahu, Jafar ya ce masa ya kai su Light Hotel da ke Zoo road. "Ina kuma za mu?" Uwani ta watsa masa tambaya. "Sayar da ke zan yi. Wallahi idan muka je kika yi mini ƙauyanci sai jikinki ya faɗa miki." Uwani ta ja bakinta ta yi gum tana kalle-kallen titi. Har cikin harabar hotel ɗin ya shigar da su, nan Uwani ta saki baki tana kalle-kalle don wani lokacin sai Jafar ya yi gaba zai waiga ya ƙwalla mata kira, reception ya tsaya ya cike duk abin da ya dace. Aka ba shi key ya tasa Uwani a gaba da ta saki ba ki tana kallon wurin. "Don Allah ina ne nan ka kawo ni kamar Dubai da nake gani a TV?" Jin tambayar da Uwani ta yi masa ga kuma mutane na kallonsu ya sa ya ce. "Eh Dubai ce." Cikin lifter suka shiga Uwani ta ji wani irin zuuuuummmm A firgice ta ƙanƙame Jafar ta saki ihu, ƙirjinta sai bugawa yake. Sai da suka tsaya sannan Uwani ta ɗan ɗago da kanta amma har lokacin jikinta bai daina karkarwa ba. "Malama sake ni." Jafar ya faɗa yana yakice Uwani. Kamar sabuwar munafuka haka Uwani ta dinga raba idanu kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci a tsorace take. Buɗe ɗakin ya yi suka shiga, a gajiye ya zube a kujera Uwani ta tashi ta fara leƙa ɗakin. "Don Allah ina muka zo Ya Jafar?" "Light Hotel." Jafar ya amsa mata a taƙaice. A zabure Uwani ta miƙe tsaye jiki na rawa ta ce, "Wallahi ba zan kwana Otal ba salon haka kawai a dinga ce mini 'yar iska." Uwani ta dubi Jafar a yamutse ta ce. "Ya Jafar ina maka kallon mutumci ashe kai ma kana cikin sahun sababbin 'yan iska ashe ban sani ba..." Jafar ya bige wa Uwani baki, cikin jin zafi ta sa hannu ta dafe bakin ta furta. "Wallahi ban yafe ba..." Ba ta ƙarasa magana ya sake bige bakinta. Uwani ta zauna a gefen gado tana watsa masa harara. Wayarsa ya zaro ya fara dannawa, Uwani ta ci gaba da zama cikin gundura don ita tsarin wurin sam bai yi mata ba. "Ni fa yunwa nake ji." Uwani ta yi maganar, Jafar ya yi kamar bai ji ba. Sai da ta maimaita sau uku amma ko ƙurar ta bai kalla ba, ta tashi ta leƙa ta window a nan ta hango mutane na zirga-zirga a farfajiyar wurin. "Bawan Allah ka taimaka mini yunwa nake ji." Uwani ta ƙwalla wa wani mutum kira da ta gan shi ya wuce da take away a hannu. "Mai farar rigar nan don Allah ka taimaka mini..." Cikin zafin nama Jafar ya ƙarasa ya fisgo Uwani. Da ƙarfi ya wurga ta kan gado yana huci ya ce. "Ke wacce irin mahaukaciya ce ne? Wallahi kika nemi ki tara mini jama'a sai na zane miki jikinki." "Ba na gaya maka yunwa nake ji ba? Wallahi ka kiyayi hukuncin Ubangiji atoh, a kan mage ma wata ta shiga wutar jahannama, ka san ni ma ka kashe ni da yunwa duk gatanka babu mai hanaka shiga Hawiya." Jafar ya yi yunƙurin kai mata duka da sauri Uwani ta zille tana dariya, tana gani ya ɗauki waya ya kira ita dai ta ji yana turanci amma ba ta san abin da yake faɗa ba. Bayan awa ɗaya sai ji ta yi an ƙwanƙwaso musu ƙofa, Jafar ya karɓi abincin ya dire. Plate ɗinsa ya ɗauka bai tanka wa matai ba, ganin haka ya sa ita ma ta sauka ta ɗauka ta fara cin abinci. Bayan ta gama babu jimawa aka kira sallar Azahar, tana idarwa ta ɓingire a akan dadduma bacci ya yi gaba da ita. Tun da Jafar ya fita sallar Azahar bai dawo da wuri ba, kusan sallar La'asar Uwani ta farka shi ma sanyin AC ne ya dame ta. Banɗaki ta shiga yin alwala tana ta jinjina lamarin ƙayatuwar banɗakin da kuma nasu ɗakinsu, bayan ta idar da sallah atamfar jikinta ta sauya ta ɗauko wasu riga da wando baƙaƙe ta saka. Sai wata farar hula da ta ɗora a kanta, ta saka hijabinta ƙarami. Jin zaman ta yi ya gundure ta don haka ta buɗe ƙofar a hankali tana leƙe-leƙe. Sai a lokacin da lura da fasalin ɗakunan duk suna kallon juna sai dai kowacce ƙofa a datse take. Tafiya ta fara yi tana kalle-kalle ba ta yi aune ba sai ji ta yi garam ƙofar ɗakin ta datse, Uwani ba ta wani damu ba ta ci gaba da tafiya har ta fita wurin wata baranda ta hangi step ɗin bene. Takawa ta fara yi a hankali har ta sauka sai ganinta ta yi ta sauka can farfajiyar wurin da ta hango mutane na kai-kawo. A kan ɗaya daga cikin kujerun harabar wurin ta zauna, a gefe ɗaya kuma swimming fool ne tsirarun mutane sun zauna suna saka ƙafarsu a cikin. Abin ba ƙaramin birge Uwani ya yi ba, abu ɗaya ne ya takurata ganin yadda wani Alhaji da ke gefenta ya zuba mata idanu da sun haɗa ido sai ya sakar mata murmushi, ko ya kashe mata ido ɗaya. Kiransa ta ji an yi a waya ya ɗauka yana barin harabar wurin. Babu jimawa ita ma ta tashi ta nufi hanyar ƙafar benen da ta sauko, wata hanya ta bi wacce take ganin kamar hanyar ɗakinsu ce. Amma sai ta ga ta gagara gane ainihin ɗakinsu, wata ƙofa ta gani a buɗe. Ta ga yanayin wurin ya yi mata kama da ɗakinsu da sauri ta tura ƙofar, turus ta yi tana kallon mutumin. Mutumin ɗazu da ta ga an kira a waya ne, ya washe mata baki yana faɗin. "Ranki shi daɗe ke kaɗai ce?" Uwani ta yi saurin kawar da kai gefe don jibgegen mutumin daga shi sai gajeren wando, ya ɗora towel a kafaɗarsa da alama wanka zai shiga. "Eh ɗakina nake nema?" Kallon tsaf ya yi mata, nan take ya lura da Uwani farin shigar zuwa hotel ce. Ba ta yi aune ba ta ji ya janyo hannunta ciki ya datse ƙofar, ya fara shafa gemu ya ce. "Ranki shi daɗe ni fa dama tun ɗazu nake ɗago miki hannu ba ki fahimta ba ne." Uwani ta fisge hannunta da sauri ta ce. "Malam ni ba 'yar iska ba ce ka buɗe mini ƙofa." Alhajin mai tumbin kuɗi ya ajiye towel ɗin a gefen gado, ya sake tunkarar Uwani ya furta. "Yarinya kada ki cuci kanki, yayyafin kuɗi zan yi miki ko awa guda ba za ki yi ba za ki kama gabanki." Ya ƙarasa maganar yana sake riƙo hannun Uwani. Uwani ta fisge tana ja da baya, Alhaji mai tunbin kuɗi ya lashe baki yana faɗin. "Ni fa tun da na yi arba da ke yawuna ya tsinke, dama tunanina ɗaya na san yadda za a yi na yi arba da ke." Alhaji tumbin kuɗi na rufe baki Uwani ta sunkuyar da kai ƙasa tana ɗagowa sai ji ya yi ta fara ɓaɓɓaka dariya. Juya idanunta ta yi ta fara wani ƙobare hannuwa cikin wata irin murya ta fara magana. "A yau za ka mutu tun da har ka taɓo mana goɗiya 'yar sarkin mayun aljanu." Uwani ta fara tunkarar Alhaji tumbin kuɗi tana wani murɗe kai gefe. A can gefen gado ta hango belt ɗinsa sai ta buga wani uban tsalle ta suri belt ɗin, daidai wurin ƙarfen ta shammaci Alhaji ta zuba masa a baya. A zabure Alhaji ya ƙandare yana faɗin. "Wash! Bayana." Uwani ta dafa hannuwanta biyu a saman kanta, tana motsi da bakinta. Ganin haka ya sa Alhaji ya saki baki yana kallonta a tsorace. "Uwar ƙwaƙwido ki ɗauke gashin kaina a yanzu, saboda mummunan hukunci za mu zartar a yanzu. Ki mayar mini da kaina babu gashi irin na wannan tsinannan da yake gabana." Uwani na gama faɗin haka ta fisge hular kanta, nan take Alhaji tumbin kuɗi ya zaro ido cikin tashin hankali ganin kan Uwani babu gashi. Uwani ta fara wani gurnani tana tunkararsa, ganin haka ya sa Alhaji ya taƙarƙare ya zuba uban ihu yana faɗin. "Wayyo Allah maman Garzali ki taimaka mini za a hallaka ni." Uwani ta maƙe wuya tana zaro harshe ta ce. "Za mu kwashe wannan tumbin naka mu zuba maka duwatsu a ciki, domin kana cin amanar Maman Garzali matarka. Zan kuma fafe ƙoƙon ƙeyarka na dura maka ruwan tekun maliya a ciki." Da sauri Alhaji tumbin kuɗi ya dafe ƙeyarsa ya zuba a guje, hawaye haɗe da majina suka wanke masa fuska. "Matso ka hau saman silin ko ka hau kan fanka, idan ba haka ba zan sa a yi sama da kai ko a nutse ƙarƙashin ƙasa da kai." Jiki na karkarwa Alhaji ya hau saman gado ya fara tsalle zai hau saman silin, idan ya yi tsalle ɗaya sai ka ji ɗass! Uwani ta zuba masa duka da belt. A galabaice ya dubi Uwani ya ce, "Don Allah ku yi mini rai wallahi a yanzu jinina zai iya hawa, ko nawa kuke so zan ba ku amma ku ƙyale ni." Uwani ta yi wani farrr da idanu, sannan ta ce. "Mu ba matsiyata ba ne, ba ma buƙatar kuɗinka Dama mu yawo muke Otel-otel muna hukunta masu hali irin naku masu lalata 'ya'yan mutane." "Wallahi har abada na daina ba zan sake ba don Allah ku yi mini rai." Uwani ta wurƙila ƙafa tana kanne ido ɗaya ta ce, "Za mu ƙyale ka amma da sharaɗin sai ka cinye sabulun wankan da ke banɗakinka, ko kuma mu farke cikinka mu tura maka 'ya'yan aljanu bakwai..." Tun Uwani ba ta gama magana ba Alhaji ya faɗa banɗaki da gudu ya ɗauko ragowar sabulun wankansa ya tura baki, yana ci yana kuka haka ya cinye sabulun bakinsa sai kumfa yake. Uwani ta suri hularta a fakaici ta riƙe sannan ta sake ɓaɓɓaka wata irin dariya ta ce. "A zo a buɗewa Goɗiyar mayun aljanu ƙofa." Ba musu Alhaji tumbin kuɗi ya buɗe mata ƙofar, jikinsa banda karkarwa da gumi babu abin da yake yi. Sai da Uwani ta fita ta sauke ajiyar zuciya don ita kanta ilahirin jikinta karkarwa yake, duk abin da take yi ƙarfin hali ne don ta lura da ta nuna masa tsoronta a fili ba abin da zai hana bai ci galaba a kanta ba. Daga ɗaki mai kallon na Alhaji tumbin kuɗi ta ji wani mutum yana yi mata ɗan kira, a shekaru shi ma bai fi sa'an Alhajin ba. Yi ta yi kamar ba ta gan shi ba gabanta sai faɗuwa yake. Ta bayanta ta ji ya fara biyo ta yana faɗin. "Haba 'yan mata kada ki yi wasa da damarki, abin da abokina ya ba ki ni zan ninka miki shi." A tunanin mutumin tun da ya ga Uwani ta fito daga ɗakin abokinsa ita ma 'yar hannu ce. Ganin haka ya sa Uwani ta fara sauri mutumin na biye da ita har dai ta ga da gaske yake ta saka gudu, tana yunƙurin shan kwana sai ta ji ta yi karo mutum. Cikin tashin hankali ta furta. "Don Allah ku taimaka mini wallahi ɗan iska ne ya biyo ni." Mutumin da kawo kansa kenan ya furta. "Haba 'yan mata ni fa ko awa guda ba za ki yi mini ba, don Allah ki bari..." Maganarsa ta maƙale sakamakon arba da ya yi da Uwani riƙe da Jafar. "Kai yaro wannan fa ba kalar yara ba ce. Don 'yan shiloli kamar su sun wuce ajinku." Cikin ɓacin rai Jafar ya furta. "Amma dai Allah wadaran hali irin na lalatattun tsofaffi kamar ku." Jin muryar Jafar ya sa Uwani ta ɗago da sauri don ko kaɗan ba ta taɓa tsammanin shi ba ne, suna haɗa ido ta riƙe shi ƙam jikinta na rawa cikin kuka ta furta. "Ya Jafar." Sai kawai kuka ya sake cin ƙarfinta. Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki turo ta Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 Free pages ɗinmu ya kusa ƙarewa🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA SHA UKU Jin yadda jikin Uwani yake karkarwa ya sa Jafar ya kwantar da ita a jikinsa ya sa hannu ya fara bubbuga bayanta, nan take idanunsa suka yi jawur saboda ɓacin rai. Ya dubi mutumin murya a dashe ya furta. "Ka san wa ka taɓa kuwa? Ka san wanne irin kuskure kake yunƙurin aikatawa. Wallahi sai na nuna maka bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne." Jafar ya ƙarasa maganar yana yunƙurin cire Uwani daga jikinsa, cikin kuka Uwani ta furta. "Tsoro nake ji Ya Jafar don Allah kada ka sake tafiya." Ajiyar zuciya Jafar ya sauke ya riƙe hannunta suka fara tafiya rai a ɓace, ganin haka ya sa Alhajin ya zuba a guje ya faɗa ɗakinsa ya datse ƙofa. Ɗakinsu suka wuce sai da Jafar ya sa key ya buɗe suka shiga, ya kai ta kan kujera ya zaunar da ita sannan ya ce. "Ki jira ji yanzu zan dawo." Fuska da hawaye Uwani ta furta. "Ya Jafar kada ka tafi ya shigo mini." Sunkuyawa ya yi daidai fuskarta ya ɗan hura mata iska ya furta. "Ba abin da zai faru da ke yanzu zan dawo kin ji." A hankali Uwani ta gyaɗa masa kai sannan ya fice. Ɗakin Alhajin ya koma ya yi bugun duniya ya ƙi buɗewa, shi kuwa Alhaji tumbin kuɗi jin ana buga ƙofar ɗakin abokinsa da ƙarfi, ya sa ya ƙara wa tashi ƙofar key sannan ya wuce banɗaki a guje jiki na rawa ya ɓuya. Ganin ba shi da niyyar buɗewa ya sa Jafar ya zaro waya ya danna lambar DPO ɗin unguwar Zoo road, da yake abokinsa ne. Nan take ya sanar da shi abin da ya faru tsakanin Uwani da Alhajin. Sannan Jafar ya sauka ƙasa ya sanar da ma'aikatan reception abin da yake faruwa da kuma ɗakin da Alhajin yake ciki. Wata mata da ke gefe nan take ta furta. "Kai malam Allah Ya yi maka albarka. Wallahi ni ma jiya da dare na ɗan fita unguwa na dawo haka wani ya dinga mini ɗan kira, da na shiga ɗaki har buga mini ƙofa ya yi ƙila ma shi ne." Jafar ya furzar da iska mai zafi ya ce. "Daga yau ai ba zai ƙara ba." "A toh ai wasu mutanen gani suke idan suka ga mutum ya kama hotel kowa ma ɗan iska ne, Allah Ya kyauta." Ba a ɗauki lokaci ba sai ga motar 'yan sanda ta ƙaraso, lokacin da suka je bakin ƙofar Alhaji sai da ƙyar ya buɗe musu ƙofa. Har ƙasa ya tsugunna yana ba wa Jafar haƙuri amma fir ya ƙi sauraronsa, yaran D.P.O bayan sun saka masa ankwa Jafar ya ce su wuce da shi zai zo daga baya. A wurin da ya bar Uwani a nan ya koma ya same ta, fuskarta ta kumbura saboda kuka. Tana ganinsa ta yi zumbur! Ta miƙe tsaye. Bai kula ta ba ya koma can gefen gado ya zauna ya dafe kansa, wani irin ɗaci yake ji a maƙoshinsa ya ɗago murya can ƙasa ya ce. "Ya aka yi mutumin nan ya biyo ki ke da na bar ki a ɗaki?" Zuciyar Uwani ɗaya ta fara masa jawabi. "Ni fa kasan ƙafata ba ta saba zaman wuri ɗaya ba, gajiya na yi da zama shi ne na fita can ƙasa na sha iska. Da na dawo sai na rasa ɗakin nan, bisa tsautsayi na faɗa ɗakin wani ɗan iska..." Uwani ta kwashe komai ta gaya masa amma ba ta gaya masa irin azabar da ta yi wa Alhaji tumbin kuɗi ba, ta dai ce masa Allah ne ya ƙwato ta bayan ta fito wannan Alhajin ya biyo ta. Tass! tass! Jafar ya sauke wa Uwani wasu tagwayen mari biyu a fuska, cikin ɓacin rai ya furta. "Uban waye ya ce ki fita? Ba ki da hankali za ki fita da waɗannan kayan?" Ganin yadda Jafar ya hargitse mata lokaci ya sa nan take jikinta ya fara karkarwa, ya rufe ta da faɗa tamkar zai rife ta da duka daga ƙarshe ya faɗa toilet ya bar ta a zaune. Bai jima ba ya fito har lokacin ransa a ɓace yake ya furta. "Ki shiga ki yi wanka za mu wuce gida yanzu." Zani uwani ta ɗauka ta faɗa ban ɗaki kafin ta fito har Jafar ya gama shiryawa, gefe da gefen fuskar Uwani har ya ɗan kumbura don har lokacin ba ta daina hawaye ba. Jafar na zaune a gefen gado ya hango Uwani ta fito don ita ta manta ko hula ma ba ta saka ba, a razane yake bin ta da kallo baki sake. Ganin irin kallon da Jafar yake bin ta da shi ya sa Uwata ta sha jinin jikinta, tana sake tunkaro shi Jafar ya zabura a guje ya nufi ƙofa yana faɗin. "Wayyo Allah! Jama'a ku taimaka mini sun biyo ni nan ma!" Da yake ya manta ya datse ƙofar haka ya yi ta murɗawa ta ƙi buɗuwa. Cikin rashin fahimta Uwani ta ɗan waiga ta ce. "Wai ya Jafar me yake faruwa ne?" Laƙwas Jafar ya yi ya zauna a ƙasa kamar mutum-mutumi yana kare mata kallon, tamkar ya ga sabuwar hallita. Uwani ta shiga goge kanta da towel ko a jikinta ta ce. "Malam ka fita zan shirya." Har lokacin Jafar mamakin Uwani yake, ya shiga tariyo abin da ya dinga faruwa a cikin dare. Uwani ta fahimci sarai in da Jafar ya dosa, ta fito da kayan da za ta saka ta sake furta. "Don Allah ka fita zan shirya." "Uwani ina gashinki?" Cikin halin ko in kula ta ce. "Dada ta aske mini tun rannan." Miƙewa ya yi ya tako gabanta sannan ya furta. "Wato iskanci ne ya sa kika dinga tsora ta ni ko? Wallahi za ki shiga hannuna da ni kike zancen." Take dariyar da Uwani ke gimtsewa ta suɓuce mata. Jafar ya saki wani malalacin murmushin mugunta yana ayyana irin azabar da zai yi mata cikin ruwan sanyi ba tare da Daddy ya gane ba. Daga haka Jafar ya fice daga ɗakin, Uwani ta saka kayanta sannan ta haɗa ragowar kayanta da ke warwatse ta saka a jaka. Ba su ɗauki lokaci ba suka shirya suka fito Jafar ya ƙarasa gaban ma'aikatan da ke reception ya biya duk abin da ya suka kashe, sannan ya yi musu sallama suka fita da yake akwai Manajan wurin da shi a ka kai Alhaji can police station. Domin a cewar Manajan Alhajin na ƙarƙashin kulawarsu dole ne su san halin da yake ciki. Lokacin da su Uwani suka ƙarasa gida mommy ta rako ƙawarta Hajiya Binta bakin gate, ganin su Uwani ya sa Mami ta yi turus tana faɗin. "Ya aka yi Jafar?" Jafar ya ɗan sosai, sannan ya gaida Hajiya Binta da ke bin sa da kallon tuhuma. "Ƙawata wai kar dai raɗe-raɗin da nake ji a kan auren Jafar haka ne?" Hajiya Binta ta tambaya tana satar kallon Uwani. Ras! Gaban Mami ya faɗi, ta ɗan basar tana ƙirƙiro murmushin yaƙe ta ce. "Haba Hajiya Binta kina ganin akwai yarinyar da Jafar zai aura a duniyar nan bayan Safna? Ai me aiki ce ya taho mini da ita daga Lagos, a bakin gada take kwana shi ne ta roƙe shi Allah-Annabi wai ta dinga yi masa aiki. Da ya sanar da ni na ce idan zai taho ya kawo mini ita, kin san ɗa na kowa ne ƙawata." Cikin gamsuwa Hajiya Binta ta bi Uwani da wulaƙantaccen kallo ta furta. "Ban da taɓarɓarewar zamani yanzu wannan yarinyar har ta isa kwanan gada, mtsww Allah Ya sawaƙe." Mami ta furta. "Amin dai, yo yaran da maza ke ba su ɗari biyar suna sa su a ɗaki ina za ki yi mamaki?" Kalaman Mami da ƙarshe da ta jefi Uwani da su ba ƙaramin zafi suka yi masa ba, don haka ko sallama bai yi wa Hajiya Binta ba ya wuce. Ita kanta Uwani kusan daskarewa ta yi a wurin jin irin munanan kalaman da Mami ta jefe ta da shi, tunanin da ta zurfafa ciki ne ya sa Jafar ya wuce ba tare da ta sani ba. A ɗan tsawace Mami ta ce. "Tsawar me kike yi a gabanmu ne?" Babu yadda ta iya haka Uwani ta ja jaka jiki a sanyaye ta wuce ciki, kai tsaye sashensu ta shiga idanunta cike da ƙwallah. Sanin Daddy ba ya gidan ya sa Mami kai tsaye ta wuce sashen su Jafar, a falo ta same su duka ta dubi Jafar ta ce. "Wai fasa tafiyar ka yi ne Jafar?" Bai ɗago ya kalle ya ba ya furta, "Eh Mami." Jim ta yi tana nazartarsa ta furta. "To haka za ka zauna ana tsorata ka har a sabauta mini kai?" Jafar ya furta. "Ai na biya ta Islama Islamic Center na karɓo magani, kuma ya ce mini za a dace In shaa Allah." Jafar shi kansa ya yi mamaki yadda ya tsara wa Mami wannan jawabin, Mami ta wurga wa Uwani mugun kallo ta ce. "Wuce mu je akwai aikin da za ki yi mini." Babu musu Uwani ta bi bayan Mami, Jafar ya kwanta a kan doguwar kujewa. Haka kawai ya ji yana kewar Safna, don haka ya zaro waya ya kira ta suka fara hira. Mami na shiga sashensu ta haɗo wa Uwani wanki duk da a lokacin magriba ta fara kawo kai, bayan gida ta zuba mata wankin ta yadda koda an yi a arashi Daddy ya dawo ba zai ganta ba ballanta ya yi mata faɗa. Kuma dama ta san ba ya gari, don haka za ta ci karenta babu babbaka akan Uwanin. Cikin wankin da Mami ta haɗo wa Uwani har da labulaye da zannuwan gado, tun Uwani na wankin cikin daɗin rai har ta fara galabaita tun da ko a wurin Dada ba ita take yin wankin kayanta ba. Lokacin da aka kira sallar magriba Uwani wucewa ta yi sashenta don ya gabatar da sallah, tafiyarta babu jimawa Mami ta zagaya ta ga wurin wayam. Sai tsirarin kayan da ta shanya ga waɗansu nan a cikin ruwa. Uwani na zaune tana zaman tahiya Jafar ya shiga ya zaune yana kallonta, a yadda ya lura da Uwani duk hatsabibanci da ƙiriniyarta ba ta wasa da sallah ko kaɗan. Hakan ba ƙaramin birge shi yake ba, yana nan zaune Mami ta shigo ko shi ba ta yi wa magana ba ta rufe Uwani da duka. Ganin dukan da take wa Uwani ba zai ƙare ba ya sa Jafar ya yi saurin shan gaban ta. "Lafiya kuwa Mami? Me ta yi miki haka?" Jafar ya furta hankali a tashe. "Lallai Jafar wannan abar har kake tarewa?" Mami ta faɗa tana sauke numfashi. Ban da kuka babu abin da Uwani take yi, ga gefen bakinta ya fashe jini na ɗiga. Saboda yadda ta galabaita kukan da take yi ko fita ba ya yi, Mami ta sake zuba mata ranƙwashi a ka tana shirin yin magana Jafar ya ce. "Mami wai me ta yi miki?" "Wanki na saka ta don iskanci za ta zube mini ta zo ta saka miji a gaba, idan uwarki ce ta saka ki za ki ajiye mata." Mami ta yi maganar tana dungurin Uwani, cikin kuka Uwani ta ce. "Sallah aka kira shi ne na zo na yi..." Da sauri Mami ta sake doke Uwani nan take bakinta ya sake fashewa. "Haba Mami, ina ce Haladu ne yake yin wanki. Kuma sallah fa ta ce ta zo..." Tas! Mami ta ɗauke Jafar da mari, ba ta tanka masa ba ta figi hijabin Uwani ta fara janta a ƙasa, ba shiri Uwani ta miƙe ta bi Mami. Saboda ɓacin rai tun ba su gama fita ba Jafar ya gegare su ya fice daga gidan zuciyarsa na suya. "Iyeee Allah Jafar watsa mini ƙasa za ka yi a ido yaushe har ka san zafin mace. Wallahi dole kai ma na ɗauki mataki a kanka." Mami ta yi maganar a ɗan tsorace don ta yi tsammanin ko wuta za ta jefa Uwani sai dai Jafar ya taya ta ba dai ya hana ba. A cikin duhu ga sauro haka Uwani ta wanke ragowar kayan da ba ta ƙarasa ba, kanta ban da ciwo babu abin da yake yi. Bayan ta gama ne ta nufi sashen Mami har ƙasa ta zube ta furta. "Na gama wankin." A yamutse Mami ta dube ta tana shirin sallamarta Shukra ta shiga ɗakin tana taunar cingam ta ce. "Ke zan saka ki aiki yanzu saura ki yi mini hauka." Uwani ta ɗaga kai a galabaice ta amsa wa Shukra. Auta da ke zaune a gefe duk sai ta ji babu daɗi, tana son ta yi magana amma tana tsoron faɗan Mami. "Kina ji Shukra na yi miki magana ba za ki iya amsawa ba?" Mami ta yi maganar tana haurin Uwani. Sai da ta goge ƙwallar idonta sannan ta rarrafa gaban Shukra ta tsugunna. "Ga Salim nan ya faka motarsa a cikin gate, za ki je ki wanke masa kuma wallahi idan ba ta wanku ba sai kin sake." Da sauri Auta ta furta. "Aunty Shukra wankin mota fa?" Shukra ta sake shan kunu ta ce, "Waya na yi da shi zai kai wankin mota ya ce ba zai samu zuwa yau ba, so don haka na ce ya zo gida za a wanke masa saboda ina son magana da shi." Cikin tausaya Auta ta ce, "To shi kenan zan ta ya ki Uwani..." "Waye ya gayyace ki? Uwar iyayi da kankanba?" Mami ta katse Auta. Shukra ce ta yi gaba Uwani ta bi bayanta a lokacin zazzaɓi har ya fara rufe ta, lokacin da suka ƙarasa Salim na cikin mota. Da ya hango su ne ya fito yana sakarwa Shukra murmushi. "You are welcome dear." Shukra ta furta tana fari da ido. "Beb an ya zan iya jiran sati ukun nan masu zuwa kuwa? Kin ga yadda kika yi kyau." Salim ya furta cikin shauƙin soyayya, Shukra ba ƙaramin daɗi ta ji ba kin kissa ta ce. "Well mu je mu zauna, ga 'yar aikin Mami za ta wanke maka mota." "Za ta iya kuwa Baby? Na ga mata ba sa wankin mota." Salim ya faɗa yana bin Uwani da ke rakaɓe a gefe. Shukra ta dubi Uwani a tsawace ta ce. "Ke ba ki iya gaisuwa ba ne?" Jikin Uwani na rawa ta tsugunna ta gaishe da Salim, sannan Shukra ta ɗan yi murmushi ta furta. "Ai in gaya maka daga motar Daddy har ta ya Jafar ita take wankewa za ka sha mamaki." Shukra da Salim suka wuce wurin wasu fararen kujeru, daga wurin da suke zauna suna iya hango Uwani da duk abin da take yi. Sai da ta goge ƙwallar idonta sannan ta ɗauki bokiti ta fara ɗebo ruwa, da yake wurin ɗiban ruwan yana da ɗan nisa da wurin wankin motar a galabaice ta fara wankin motar har ta gama. Gaban Shukra Uwani ta je ta tsaya ta ce, "Na gama wankewa." Shukra ta bi ta da harara sannan ta ce. "Matso nan." Ba musu Uwani ta matsa gaban Shukra, da ƙarfin tsiya ta fisgo Uwani har sai da ta bugu da ɗan ƙaramin table ɗin da ke gabansu ta ce. "Don ubanki ke ba ki da ladabi ba za ki iya tsugunnawa ba?" Shukra ta ƙarasa maganar tana zuba wa Uwani ranƙwashi. "Haba Beb da kin ƙyale ta kin san irin yaran nan ba wani tarbiyya suke samu ba, so don sun yi haka ni ba zan yi mamaki ba." Salim ya faɗa a ɗan ƙyamace yana duban Uwani da ta gama jiƙe wa da ruwa sharkaf. "Dallah tashi ki ba ni wuri kina tafe da baƙi kamar na zunubi." Dariya sosai Salim ya yi jin abin da Shukra ta faɗa ya furta. "Wai yaushe kika koyi masifa ne love?" "Haba ka rabu da ni na tsani yarinyar nan wallahi." Uwani na laɓe a ta bayan fulawiyin da ke zagaye da harabar gidan, takaici ya mamaye zuciyarta. Wani tunani ne ya faɗo mata don haka da sauri ta zagaya can bayan gidan, ta ɗebo irin manyan bokitan fentin nan guda biyu waɗanda ta gama wanki da su. Sai da ta yagi wata igiya ta haɗa hannuwansu ta ɗaure, sannan ta saki murmushin mugunta. Cikin sanɗa ta fara tafiya ta cikin fulawoyi, a daidai bayan su Shukra ta tsaya ta ji Salim yana faɗin. "Haba ke dai Baby ba kya mantuwa, wannan fa mahaukacin ma shammatata kawai ya yi amma yadda nake ƙaunarki akwai abin da zan ga zai cutar da ke na gudu ban taimaki rayuwata ba, ke ce fa rayuwata ke ni fa idan za ki rayu da farinciki zan iya sadaukar da komai ciki kuwa har da numfashin da nake zuƙa." Shukra ta rangwaɗa kai cikin farinciki, tana shirin ba shi amsa Uwani ta saki murmushi duk da zazzaɓin da ke jikinta. Sai da ta daidaita saitin kansu sannan ta ɗaga bokitan fentin hannunta, ta kifa musu a kansu ta saka iya ƙarfinta ta danne saman ta yadda ba za su iya fisgewa ba. Salim da abin ya haɗe masa biyu ga zafin hula ga na bokiti ya ware murya cikin ihu ya ce. "Wayyo Allah wuyana!" "Wayyo kaina, Baby kana ina!" Shukra ta faɗa a ɗimauce. Daga Salim har ita sai ɗaga hannuwa suke cikin neman taimako. Sai da Uwani ta ga sun fara galabaita sannan ta fisgo hannun bokitin ta baya, da yake ƙafafuwansu na ƙasan table ɗin da ke gabansu faɗuwar da za su yi ta baya sai suka taho da table ɗin da ƙafafuwansu. Uwani na ganin za su kai ƙasa ta yi saurin matsawa a guje, sai ji kake rugugum! kacacar kofuna da ruwan jarkar duka sun watso kansu. Ga bokiti ya sarƙafe su ga kuma ƙafafuwasu sarƙafe a cikin table, Uwani ta laɓe a cikin shukoki tana dariya ƙasa-ƙasa don duk ƙwaƙwar mutum ba zai gano da mutum ɓoye a wurin ba. Da ƙyar Salim ya samu ya zaro ƙafarsa daga cikin Table, ya tashi zai zuba a guje Uwani da ke laɓe ta sake fisgo shi da yake igiyar tana hannunta. Daɓar Salim ya koma ya faɗi hankali a tashe ya ce. "Jama'a a taimaka mana wallahi jana ake yi." Shukra ce ta yunƙura ta tashi a guje saboda tashin hankali ko yunƙurin cire bokitin ba ta yi ba, ita da Salim suka zuba a guje a daidai lokacin Jafar ya shigo harabar gidan. Turus ya yi ya ɗan fara ja da baya ganin ƙafafuwan mace da namiji suna tafe da bokiti a kai, da yake ba sa ganin gabansu yana ganin sun tunkaro shi ya zube takalmansa shi ma ya shige a guje yana ihun. "Wayyo Allah! Lado kana ina?" Jin ihun Jafar ya sake ruɗa su Salim, a wannan lokacin Lado ya zagayo da buta a hannu shi ma turus ya yi yana kallon ikon Allah. Da ƙyar Salim ya samu ya cire bokitin kansa, hular ta faɗi can gefe. Dama takalminsa na cikin ƙasan table ya jima da fita, iya ƙarfinsa ya tattara ya fita a guje yana faɗin, "Jama'a ku duba mini kaina idan yana gangar jikina." Sai a lokacin Lado ya gane shi, ya bi bayansa yana faɗin. "Alhaji ka bar motarka." Lado na ƙarasawa bakin gate ko ƙurar Salim bai gani ba sai agogonsa da links ɗin hannun rigarsa da suka zube a wurin. Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki turo ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 idan littafi ya kammala za ki turo 800 Free pgs ɗinmu ya kusa ƙarewa🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA SHA HUƊU *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 A sanyaye Lado ya ɗebo agogo da links ɗin Salim ya dawo cikin gidan, sai dai yana shiga ga wutar harabar wajen ta ɗauke. Ga kuma ƙarar duka da ake yi wa Shukra tana ihu, zuwa can kuma sai ya ji an yi wurgi da bokiti an zuba cikin gida a guje. Gudun kada abin da ya same su, shi ma ya zo kansa ya sa Lado ya shige ɗakinsa ya danno ƙofa ya rufe don shi kansa bai manta abin da aka yi masa a tsakar dare ba. Da gudu Uwani ta bi bayan Shukra tana gurnani tana zabga mata igiyar a baya har Shukra ta fara kama ƙafar bene Uwani ba ta daina dukanta ba, tana hawa sai ga Shukra na rarrafe tana kuka saboda tashin hankali. Sai da ta ga Shukra ta shige sannan Uwani ta yi saurin ɗebe bokitan ta mayar da su wurin da suke, ta je ta ɗaga table ɗin ta mayar da ruwan jarkokin kai sannan ta koma ta kunna ƙwan fitilar harabar wurin ta wuce sashenta. A lokacin da ta shiga sashenta shiru babu motsin Jafar, ta zube a kan kujera kanta na matsanancin ciwo kamar zai tsage gida biyu. Uwar ɗakinta ta wuce don ta sauya kayan jikinta saboda rawar ɗarin da take yi, ɗrower kayanta ta buɗe tana shirin miƙa hannu ta yi ido biyu da Jafar tsugunne a cikin. Uwani ta basar kaman ba ta san abin da ya faru ba ta ce, "Kai kuma Ya Jafar mene ne haka?" Jafar ya fara wuri-wuri sannan ya ce. "Wai Uwani ke ce kika zama biyu ko ya aka yi?" Jafar ya wurga mata tambaya. "Wai me ka mayar da ni ne ya Jafar? Ni fa yanzu na gama yi wa saurayin Shukra wankin mota bayan na gama yi wa Mami wanki..." Cikin sauri ya katse ta. "Wankin me? Ke kika wanke wa Salim mota? To su waye na gani da bokiti a kansu suna ihu?" Uwani ta wara hannu ta ce. "Ni kam ban sani ba, ƙila dai mutanen gidan ne suke son buɗe maka ido." Jafar ya yi fakare yana nazari, abu ɗaya ne ya fi tsaye masa a rai wai Uwani ce ta wanke wa Salim mota. A fili ta ji ya furta, "Dole sai na ɗauki mataki a kanta." Uwani ta yi saurin tambayarsa. "Wace ce?" Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya furta. "Babu komai." Saboda tsabar gajiya Uwani na sauya kaya ta ɗauro alwalar Isha'i ta gabatar da sallah, a nan kan dadduma bacci ya yi awon gaba da ita. A yadda ya ga tana sauke numfashi sama-sama ba ƙaramin tausayi ta ba shi ba, ya ƙarasa ya cire mata hijabin ya ji jikinta ya ɗauki zafi zau! Cikin jakarsa ya duba ya ɗauko Paracetamol, ya jima yana tashinta sannan ta tashi ya ba ta magani. Duk yadda ya yi da ta tashi ta ci abinci ƙi ya yi, ya rabu da ita ya haye gado ya kwanta. Shukra da rarrafe ta ƙarasa falon Mami, babu ɗankwali ballantana mayafi ko takalmi, a razane Mami ta fara tambayar Shukra. "Ke Shukra lafiyarki kuwa?" "Mami ki ɓoye ni bokiti ne, wallahi bokiti ne ya danne mu ni da Salim." Da mamaki Mami ta ce, "Kamar ya bokiti ne Shukra? Shi bokiti mutum ne da zai iya motsi har ya danne ku. Wai ma ina ɗankwalinki?" Shukra fuska da ta gama jagulewa da makeup da hawaye ta zayyanewa Mami duk abin da ya faru, Cikin damuwa Mami ta ce. "Ni fa wallahi ina zargin yarinyar nan tana da Aljanu, mu dai tun da muka tare babu wani abin tashin hankali da muka taɓa gani. Amma tun ranar da yarinyar nan ta zo gidan nan masifar yau daban ta gobe daban, yanzu bala'in har ya kai kina hira ke da Salim ana razana ku? Gaskiya dole a san abin yi." Daga haka Mami ta shiga lallashin Shukra, da ƙyar a daren ranar Shukra ta yarda ta kwana a ɗakinsu. Da yake Daddy ba ya gari ya sa asubar fari Shukra ta koma ɗakin Mami bayan ta yi sallar asuba ta koma ta kwanta. Washgari Tun bayan sallar asuba Uwani da Jafar har sun koma bacci, suka ji bugun ƙofa. Jafar ne ya je ya buɗe da mamakin mai buga musu ƙofa da farar safiya. Karo ya kusa yi da Mami a ɗan duburburce ya ce. "Mami ke ce tun yanzu?" Mami ta ƙare masa kallo ta ce, "Eh ni ce, ina Uwani take?" Jafar ya ɗan sosa kai ya ce. "Tana ciki bacci take yi." "Ciki ina? Uwar ɗaki?" Jafar ya gyaɗa kai. Cikin sauri Mami ta ce, "To kai kuma a ina ka kwanta?" A ɗan kunyace Jafar ya ce, "Ni ma a ciki na kwanta..." "Laha'ilaha'illallahu Jafar tun ba a je ko ina ba?" Salatin Mami ya katse shi. A ɗan duburburce ya ce. "Am ai ita a ƙasa take kwana ni nake kwana a kan gado." A fili Mami ta sauke ajiyar zuciya tana murmushi ta wuce cikin ɗakin. Yadda Jafar ya faɗa mata haka abin yake, bacci Uwani take sosai a ƙasa saboda gajiya. Mami ta ɗauki ruwan jarkar da ke kan mudubinta ta sheƙa mata, a zabure ta tashi tana waige Mami ta taɓe baki ta ce. "Ki zo ki wuce kitchen za ki taya Inna haɗa breakfast, kin saki baki kina bacci ai duk gidan nan babu bawanki da zai dafa miki ki dinga ci." Jafar kamar ya yi magana sai dai kuma ya yi shiru, tun da yake bai taɓa samun saɓanin da mahaifiyarsa da har za ta mare shi ba, don haka ya kawar da kai har Uwani da Mami suka fice daga ɗakin. Suna tafe Mami ban da masifa babu abin da take mata, kai tsaye kitchen suka wuce. A lokacin Inna har ta fara haɗa kayan breakfast, suna shiga Mami ta dubi Inna ta furta. "Inna daga yau Uwani za ta dinga zuwa tana ta ya ki haɗa kayan breakfast." Inna ta washe baki cikin jin daɗi ta ce. "Allah Ya taimaki Hajiya, ina matuƙar godiya. " Uwani da har lokacin bacci bai gama sakinta ba, ta fara murza ido. Ba ta yi aune ba sai jin ranƙwashin Mami ta yi a kanta ta furta. "Kin ga dai ta hanyar da na biyo da ke, wallahi kika kuskura kika bi ta ƙofar ciki daidai da rana ɗaya kika haɗa ni da Dadyn yara sai ranki ya yi mummunan ɓaci." Cikin damuwa Uwani ta amsa mata, Mami har za ta fita ta juyo ta ce. "Idan kuma kin gama ki same ni a falo." Mami na fita Uwani ta jingina kai da bango, lokaci ɗaya hawaye ya fara ziraro mata. "Yarinya a wannan lokacin kuka ba na ki ba ne, shi wannan aikin da kika ga Hajiya ta kawo ki mu dinga yi gata ne take yi miki. Saboda duk macen da ba ta iya girki ba wallahi ta faɗo a wurin miji, ki ci gaba da haƙuri watarana sai labari." Inna ta yi maganar ƙasa-ƙasa. Kukan da Uwani take yi ya yawaita jin kalaman Inna ya sa ta furta. "Wallahi ni kam na gaji Inna, gara na koma wurin Dada ni ban saba da wannan wahalar ba." Sai da Inna ta ɗan leƙa bakin ƙofa sannan ta sake ƙasa da murya ta ce. "Ita dama rayuwar aure ai takan zo wa bawa da al'amura mabanbanta. Ni na ɗauke ki tamkar jikata duk abin da yake damunki ki dinga samuna a fakaice kina gaya mini, amma kada ki bari kowa ya fahimci haka don gudun mu samu matsala ni da ke." Uwani ta ji daɗin yadda Inna ta amshe ta hannu bibbiyu, don haka ta share hawayenta ta fara taya ta duk abin da ya dace. A cikin aikin da suke yi ne Inna ta fahimci sam Uwani ba ta iya wani girki ba, hatta aikin ma wani abin sai ta koya mata. Sai kusan tara saura sannan suka kammala komai, don har wanke-wanke babu abin da ba su gama ba. Uwani ce ta bi Inna dianing tana ganin yadda take yin komai, lokaci ɗaya Uwani ta nemi duk ƙuncin da take ciki ta rasa. Suna gab da barin kitchen ɗin ne Mami ta dawo tana bin Uwani da harara, ta dubi Inna ta ce. "Idan kun ƙarasa aikin ki ɗebo mata gero kwano ɗaya ta surfa, ta niƙe mini shi yau furar daka nake sha'awa." A sanyaye Inna ta amsa, Mami ta wuce ta buɗe tukwanen wurin, ganin abincin da Inna ta rage kusan na mutum bibbiyu ne ya sa Mami ta furta. "An kai wa Lado abincinsa ne?" Da sauri Inna ta amsa. Mami ta sake haɗe fuska ta ce. "Wannan abincin ai ya yi miki yawa Inna zuba mini a wancan plate ɗin." "Dama ni da Uwani na rage mana..." Mami ta yi saurin katse Inna. "Uwani idan ta gama za mu rage mata abincinta a wurinmu." Inna babu yadda ta iya haka ta ɗauki plate ta zuzzuba kamar yadda Mami ta buƙata, kusan shekararsu Takwas tana yi wa Mami aiki ba ta taɓa ganin ta yi mata iyaka da abinci ba sai yau, a ranta ta jinjina ƙarfin ƙiyayyar da take yi wa Uwani. Uwani tana kuka haka ta karɓi geron ta nufi harabar gidan tana dakawa, tun ba a je ko ina ba hannunta ya fara kanta ga turmin dakan ba shi da girman kirki don a surfe ma sai da ta raba shi gida huɗu sannan ta gama dake shi. Tun Uwani na cikin inuwa har rana ta same ta don sha biyun rana a lokacin ta kusa, tana nan tana daka su Shukra suka fito cikin shirinsu gwanin birgewa. Auta ce ta ƙarasa wurinta da sauri ta ce. "Uwani me kike yi haka ne?" Uwani ta share hawayenta. Tausayin Uwani ya kama Auta, a sanyaye ta ce. "Ki yi haƙuri Uwani In shaa Allah Mami za ta gane abin da take ba ta kyautawa, unguwa za mu yanzu wallahi da na taya ki." Uwani ta gyaɗa mata kai sannan ta wuce wurin su Shukra da har sun fita bakin gate. Fitar su Shukra ba jimawa ita ma Inna ta zo ta yi wa Uwani sallamar za ta je kasuwar Garu, Mami ta aike ta yin cefane. Ita kanta Inna ta so taya Uwani sai dai tana tsoron kar ta je ta yi abin da za ta bar aikinta, don da kuɗin albashinta take samun na rufin asiri. Lokacin da Uwani ta gama ta gama galabaita, ga yunwa ga kuma gajiya. Can kitchen ta je ta ajiye wa Mami garin geron saboda ba ta san yadda za ta sarrafa shi ba, ta fito za ta shiga ta ƙofar falo ta hangi wani tafkeken jangwalagwada. Har a fili sai da Uwani ta saki murmushi, ta ɗauko tsumma a kitchen da sauri ta ƙarasa wurinsa ta yi A'uzubillahi sannan ta damƙe shi da hannunta, a wannan karon ta ci alwashin yadda Mami ta azabtar da ita to ita ma sai ta rama. Har ta gama tsara komai koda ta kwaɓe mata tana gamawa Kura za ta yi wurin Dada, kuma ko kashe ta za a yi ba za ta dawo gidan ba. Cikin sanɗa take tafiya har ta shiga falon babu motsin kowa daga can ɗakin Mami ta fara jiyo muryarta sama-sama da alama waya take yi. Ta matsa a hankali da niyyar ta buɗe ƙofar ta zura mata ƙadangaren ta ji Mami na faɗin. "Haba Hajiya Karima kin gan ni fa na tuɓe kaya yanzu haka wanka zan shiga, don Allah ku jira ni. Kin san yadda nake bala'in son haɗuwa da matar DC kuwa? Kin san fa duk in da harkar manya take ba ma sanya da ita." Uwani ta saki murmushi da ta tuna tsiyar da za ta ƙulla wa Mami. A kan kunnen ta Mami ta gama wayar ta faɗa banɗaki, sai da ta tabbatar da wankan Mami ya fara nisa sannan ta buɗe ƙofar ɗakin a hankali ta shiga. Ƙofar banɗakin ta nufa sai ta fara murɗa ƙofar da sauri-sauri, daga ciki Mami na saɓa sabulu a fuska ta ji ana murɗa ƙofar. Mamaki ne ya kamata don ta san su Shukra ba sa nan, kuma ko suna nan ba za su buɗe mata banɗaki tana ciki ba. "Waye a nan?"Mami ta tambaya a hassale. Uwani ta kausashe murya ta ce, "Sarki ne ya zo da kansa ba aike ba." Da mamaki Mami ta furta. "Sarki wane iri? Kai waye da har za ka tsallake ko ina ka shigo ɗakin matar aure, kuma har ka nemi buɗe ni a banɗaki." "Sarautar ce haka! Kuma na aure ki daga yau, tun da na samu sukunin mai gidanki ba ya nan. Dama tun ranar da aka yi maganar auren ɗanki Jafar ni ma na kai kuɗin aurenki, yanzu haka kuma na biyo ki ne domin na ɓarje amarci." Uwani ta ƙarasa maganar dariya na son ƙwace mata. A hargitse Mami ta ce. "Kai malam wai waye kai ne ma? Ba ka da hankali za ka ce ka na son matar aure?" Uwani ta sake kausashe murya ta ce. "Ni dai babban burina ki ba ni haɗin kai domin ni matashin saurayi ne dal, soyayya ce kawai ta sa na tsaya a kanki. Amma kada ki yi mamakin kasancewa ta wata halitar da ba irin taki ba." Uwani na gama faɗar haka ta buɗe ƙofar a hankali ta wurgar wa Mami Jangwalagwadan sannan ta janyo ƙofar da ƙarfi ta rufe, da yake da key a jikin ƙofar nan take Uwani ta murza key ɗin ta cire shi ta ajiye a gefen gadon Mami. Lokacin da Mami ta ji abu ya sauka a kafaɗarta da sauri ta hau kiciniyar wanke kumfar fuskarta. Hannunta ta kai ta shafo kafaɗarta bayan ta wanke fuskarta, wani irin ƙadabarbar ta ji take jikinta ya hau karkarwa. Ta yi ta maza ta yi wurgi da shi, sai a lokacin idonta ya sauka akan tafkeken ƙadangaren. Da yake shi ma ya galabaita nan take suka fara 'yar tsere da Mami a banɗaki, duk yadda Mami ta so buɗe ƙofar sai ta gagara. Cikin Kuka Mami ta ce. "Wayyo Allah Lado, Jafar kana ina ka kawo mini ɗauki." Uwani ta gimtse dariyarta, ta sake matsa wa jikin ƙofar ta ce. "A yanzu babu mai iya taimakonki domin amarci na zo ci. Kuma daga yanzu ni fa zan dinga rikiɗa har zuwa surar mutane ina kawo miki ziyara." Uwani na gama faɗar haka ta sulale ta fice daga ɗakin, cikin sauri ta zagaya ta wuce sashenta. Jafar ta gani ya yi ɗaiɗai a falo yana bacci, da alama kallo yake yi bacci ya yi awon gaba da shi don ga remote nan a gefensa. A hankali ta wuce cikin ɗakinta ta faɗa kan gado tana sauke ajiyar zuciya, ƙugin da cikinta ke yi ne ya sake ankarar da ita yunwar da ke cin ta. Kitchen ta faɗa ta fara duba tukwane, ta ci karo da guntuwar Indomie da Jafar ya ci ya rage. Tukunyar ta ɗauko ya zuba shayi ta koma falo ta zauna ta ci, sannan ta buɗe bokitin dubulan ɗin ta ta ɗebo alkaki da dubulan na gararta ta baje a ƙasa ta ci gaba da loda wa cikinta. Tana cikin ci suka ji bugun ƙofa kamar za a ɓalle ta. "Ranka ya daɗe! Ranka ya daɗe akwai abin da yake faruwa a sashen Hajiya." Jafar shi da Uwani kusan lokaci ɗaya suka miƙe a zabure, da sauri Jafar ya buɗe ƙofar ya ga Lado da Baba tsoho, a ɗimauce ya ce. "Lafiya Lado?" "Ranka ya daɗe bugun ƙofa nake ji a sashen hajiya kuma idan aka buga bayan wani lokaci sai na ji shiru, kuma sama-sama nake jiyo muryar Hajiya kamar tana kuka." Jafar tun bai gama jin kalaman Lado ba shi da Uwani suka zuba a guje suka yi sashe ta, ganin haka ya sa Lado da Baba tsoho suka rufa musu baya. Jafar na zuwa ɗakin Mami ya nufa, abin mamakin komai tsaf yake babu wata hayaniyar tashin hankali. Wani rin numfarfashi suka ji a cikin banɗaki, da sauri Jafar ya dinga buga ƙofar yana kiran sunanta. Bugun da Jafar yake yi ne ya sake farfaɗo da Mami daga suman da ta yi, wanda ta yi suma a cikin banɗakin babu adadi. "Jafar! Wayyo Jafar ka shigo ka taimaka mini, wallahi ƙadangare ne zai haike mini." Mami ta yi maganar a galabaice don saboda wahalar da ta sha ko motsin kirki ba ta yi. Da ƙarfi Jafar ya dinga buga ƙofar amma a ƙame take ƙyam ta ƙi buɗuwa, "Ranka shi daɗe wannan ba shi ne mabuɗin na?" Lado ya ɗago key ɗin da ke kan gadon Mami. Da sauri Jafar ya karɓa ya buɗe yana buɗewa ƙadangaren ya yo bakin ƙofar a guje, ganin haka ya sa daga Lado har Jafar suka ɗiba a guje. Sai da suka ga ya shige ƙarƙashin gado sannan suka fara leƙowa, Mami da rarrafe da jan ciki ta fara tahowa Baba tsoho ya tunkari ƙofar banɗakin da niyyar taimaka mata, yana leƙawa ya hangi Mami tumɓur da sauri ya juya da baya yana faɗin. "Kai a'uzubillahi wannan lamari da muni yake." Baba tsoho ya nufi bakin ƙofa su Jafar na ganin yadda ya dawo jiki a sanyaye Lado ya je zai shiga da sauri Baba tsoho ya girgiza kai ya furta. "Ummm-ummm ku dawo Lado abin babu kyawun gani." Lado na zuwa ya ci karo da Mami na jan ciki, Mami da take a yunwace da neman taimako ta fara jan ƙafar wandon Lado tana faɗin. "Ku fitar da ni daga gidan, idan ba haka ba za su kashe ni." Ganin yanayin da Mami take ciki ya sa Lado ya fisge a guje yana faɗin. "Subhanallahi wannan lamarin ya munana Baba tsoho me ya sa ba ka buɗan aiki ba? Haka kawai zan ƙone idanuna." Jafar ya nufi wurin banɗakin, kamar haɗin baki Lado da Baba tsoho suka yi wata uwar sufa suka dafe kafaɗun Jafar suna faɗin. "Wallahi al'amarin akwai muni Jafar kada ka shiga." A ƙufule Jafar ya fisge ya ce. "Ni da uwata ne za ku yi mini iyaka? Duk halin da take ciki ni ba zan guje ta." Jafar ya fisge da ƙarfi ya tunkari wurin da Mami take. Cikin hukunci Ubangiji gobe ne za mu kammala Free pages ɗinmu, idan kina buƙatar ci gaba za ki biya 500 ta wannan Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar ta wannan lambar 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye. SHAFI NA SHA BIYAR *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Jafar na shiga da ya ga a halin da Mami take ciki turus ya yi, da sauri ya juya cikin damuwa ya dubi Uwani ya ce. "Maza ki shirya ta za mu wuce asibiti." Uwani da ke gimtse dariyarta ta wuce sumi-sumi kamar sabuwar munafuka ta ƙarasa wurin Mami da ke sharɓe a ƙasa. Baba tsoho shi da Lado dama tuni suka fito harabar gidan, suna nan tsaye Jafar ya fito abin duniya ya dame shi. "Kai Jafaru, wai ya aka yi ƙadangare ya shiga har banɗakin mahaifiyarka? Ko dai ture aka yi mata?" Jiki a sanyaye Jafar ya ce, "Wallahi Baba tsoho ban da masaniya, ka na gani dai kune kuka kira ni ina ɗaki." Daga haka gabaɗaya suka yi jigum-jigum. Abin ka da mai ƙiba Uwani da ta ɗago Mami sai dai ka ji ta sake komawa sharaf, kuma har lokacin idanun Mami a rufe suke. Da ƙyar Uwani ta samu ta ja Mami a ƙasa kamar rago, ta ƙarasa da ita bakin gado tana zaunar da ita a kai ta sake tafiya sharaf, kayan da ta gani a gefe wanda Mami ta ɗauko za ta sa su ta fara dubawa. Rigar maman Mami ta ɗauko ai kuwa Uwani tana ɗaga wa ta faɗi a wurin tana ƙyaƙyata dariya saboda girmanta, sai da ta yi mai isarta sannan ta miƙe ta fara kiciniyar saka wa Mami. Da ƙyar Uwani ta samu ta shirya Mami sannan ta leƙa waje ta kira Jafar, yana zuwa nan take ya kama Mami ita ma Uwani ta kama ta suka fita ita. A kujerar baya suka saka Mami, Jafar ya kunna motarsa suka wuce asibiti. Suna zuwa asibiti da sauri aka karɓi Mami aka shiga da ita, aka fara ba ta agajin gaggawa. Sai da Jafar ya ga Mami ta samu bacci sannan ya samu sukunin kiran Daddy ya sanar da shi halin da ake ciki, a nan take yake sanar da shi yana hanyarsa ta dawowa. Lokacin da Mami ta farka gabaɗaya iyalanta na wurin, Daddy ne ya matsa gaban gadon ya fara yi mata sannu. Da wani irin kallo take bin sa ta yunƙura ta cukumo wuyan rigarsa a zabure tana faɗin. "Wallahi ba zan aure ka ba, ni ina da aure har da 'ya'yana!" Da sauri Daddy ya riƙo ta, Mami ta ɗago kai tana ƙare masa kallo sai gani suka yi Mami ta sake tafiya luuuu a sume. Har rige-rigen fita kiran Likita suke yi, babu jimawa Dr Nura ya shiga cikin shigarsa ta likitoci. Sai da ya gama jin bayaninsu sannan ya ce gabaɗaya su fita, don yana son ba ta kulawa babu buƙatar hayaniya. Daddy ya so zama don ciwon na Mami ba ƙaramin tsoro ya ba shi ba amma Dr ya ce ya fita. Wata allura ya yi wa Mami ba ta fi minti ɗaya ba ta sake farfaɗowa, tana daga kwance ta ga Dr Nura tsaye a kanta cikin fararen kaya ga farin gilas maƙale a idonsa. "Wato wannan karon rikiɗe mini ka yi zuwa wannan surar kenan? Wannan fa idan ba da gaske na yi na ƙwaci kaina ba sai ya illata ni ya cuci iyalina." Duk waɗannan maganganun Mami na yin su a cikin zuciyarta ne, ta dai kafe Dr Nura da kallo ko ƙiftawa ba ta yi. Ta fara motsa baki a hankali tana biya Ayatulkursiyyu. "Sannu Hajiya! Yanzu yaya kike jin jikin na ki?" Dr Nura ya tambaye ta yana gyara tsayuwarsa. A hankali ta yunƙura ta tashi zaune tana ɗan dafe kanta, cikin shammata Mami ta suri dogon ƙarfen nan da ake maƙala ledar ƙarin ruwa a jiki ta shiga zungura masa tana kwaɗa masa. Idan Mami ta karanta Ayatulkursiyyu ta tofa masa sai ta ɗaga ƙarfen ta ba shi ƙwal. Hankali a tashe Dr Nura ya shige can kusurwar ɗakin yana faɗin. "Help! Help! Help!" Mami ta sake zungura masa ƙarfen tana faɗin. "Wato don ubanka har surar Nasara kake rikiɗewa ai wallahi yau ko ni ko kai." Dr Nura ganin neman agajin da yake yi da harshen turanci ba zai kai shi ba, ya sa ya taƙarƙare cikin ihun tashin hankali ya ce. "Wayyo Allah! Jama'a Patient ɗin nan za ta halaka ni." Su Daddy na daga waje suka jiyo ihun Dr Nura, da gudu suka taho za su buɗe ƙofar, sai dai da yake Mami na jingine da ƙofar tana jin alamun za a buɗe ta sake danna ƙofar da ƙarfi tana zungurin Dr. Ganin Mami na niyyar illata shi ya sa ya faɗa ƙarƙashin gadon asibitin, da ƙyar su Daddy suka turo ƙofar suna ganin ta da ƙarfen suka shiga kallon-kallo suma suna ja da baya. Daddy ne ya murɗe hannun Mami ya karɓe ƙarfen ya ajiye, sororo ta yi ta fara kallonsu ɗaya bayan ɗaya sannan ta ce. "Daddyn yara da gaske kune? Ina ne nan?" Kafin Daddy ya ba ta amsa tuni Dr Nura ya yi wata irin sufa irin ta jaruman indiya ya fice daga ɗakin, glass da takalmansa kusan lokaci ɗaya suka yi tsalle sama suka zube a tsakar ɗakin sai dai hakan bai sa ya tsaya ko waige ba ballana ya ɗebi abin sa. Kan gado Daddy ya zaunar da ita yana yi mata sannu, sai ji suka yi ta fashe da kuka tana faɗin. "Daddyn yara ni dai daga nan ka wuce Kura da ni, har abada ba zan sake kwana a gidan can ba." Kamar ƙaramar yarinya Daddy ya shiga lallashinta sai da ta yi shiru sannan ya tambaye ta ainihin abin da ya faru. Tiryan-tiryan Mami ta sanar da shi abin da ta ji da kuma shigowar ƙadangaren, don ita ko shigar su Jafar ba ta sani ba saboda ta yi suma ya fi bakwai a cikin banɗakin. A yanzu shi kansa Daddy ya fara yarda da cewar gidan ba su kaɗai ba ne, saboda ya sake kwantar mata da hankali ya ce ya amince za su koma can da zama. Uwani na rakuɓe a gefe ta yi zuru tana ƙarewa fuskar Mami kallo, tana mamakin yadda Mami ta zabge ta zuƙe a wuni guda, suna haɗa ido ta doko mata harara ba shiri Uwani ta janye idonta gefe. Daddy da kansa ya koma kiran likitan da zai sake duba Mami duk da ya lura ciwon ba na asibiti ba ne, da ƙyar ya samu Dr Samira ta je ta duba Mami ta saka mata ƙarin ruwa da allurai bayan wani lokaci aka sallame ta. Su Shukra ko kaɗan ba su so komawa Kura ba don dai babu yadda suka iya ne, ita kuwa Uwani murna fal ciki. Daddy ne ya kwashe su suka ɗebo kayan sakawarsu. Mami kuwa fir ta ƙi yarda ta shiga gidan sai a mota suka bar ta. Su Shukra sun ɗauki hanyar Kura babu jimawa Salim ya kira ta a kan zai je ya ɗauki motarsa, bai dai gaya mata ba amma a cikin ransa ya ƙissima ba zai sake zuwa gidansu ba har zuwa lokacin da za a ɗaura musu aure. Adaidaita sahu ne ya sauke shi a ƙofar gidan Daddy, gaban Salim ne ya fara faɗuwa a hankali ya yi ta maza ya ƙarasa jikin gate ɗin ya fara ƙwanƙwasawa. Daga cikin gidan Lado ya furta. "Waye nan?" "Lado ni ne." Zuro kai Lado ya yi yana ganin Salim ya washe baki ya ce, "Allah Ya taimake ka, yau kaine da rana tsaka." Salim ya miƙa masa mukullin motarsa ya ce. "Shiga ka tuƙo motata ka fito mini da ita." Sororo Lado ya yi ya furta. "Ranka ya daɗe ni da ko mashin ban iya tuƙawa ba, ina ni ina tuƙa mota?" "Lado amma gidan nan ba ku kaɗai ba ne a ciki, ka na gani dai rannan aka so tafiya da mu a bokiti ban da ƙarfin addu'armu da ta iyaye da tuni wani zancen ake ba wannan ba." Lado ya yi jim sannan ya ce. "Ranka shi daɗe naka ai mai sauƙi ne." To yau dai in faɗa maka tik da ka sani haka ƙadangare ya tarfa Hajiya tumɓur tana wanka. Kai yanzu haka ma suna can hanyar Kura don gabaɗaya Hajiya ta rikice, ban da sha'anin iska ina ka taɓa jin ƙadangare ya auri mutum? Wai ƙadangare ne fa yake ce mata amarci zai sha da ita, ina ka taɓa ganin ƙadangare na magana?To Kai kuwa ma a shekarun Hajiya ban da neman cika wa da imani me take nema a wurin namiji ballantana ƙadangare? To ɗazun nan sun zo ɗiban kaya za su wuce Kura Uwani ta kwashe komai ta faɗa mini." Take cikin Salim ya sake kaɗawa, ganin ya ɗan fara ja da baya Lado ya ce. "Ni ma fa Baffa nake jira ya zo a yi wacce za a yi, idan har ƙadangare zai auri Hajiya ni waye da ƙangaruwa ba za ta aure ni ba. Haka kawai ina zaune ta murƙushe ni cikin dare babu mai ceton rai." Salim ya zaro ido ciki a tsure ya ci gaba da ja baya. Lado ganin haka ya sa ya ce. "Ranka shi daɗe ina za ka je ne? Ka shigo ka ɗauki motarka mana." Salim ya zabura a razane ya furta. "Allah Ya tsare ni wallahi, zan aiko a ɗaukar mini ita daga baya don ita kanta motar kafin na fara hawa sai an yi mata sauka biyar." Daga haka Salim ya juya ko sallama bai yi wa Lado ba yana zuba sauri. Da zuwan su Mami Kura ba a ɗauki lokaci ba, labarin abin da ya faru da ita ya watsu cikin gidan gabaɗaya. Facalolinta sai zuwa suke duba ta, wanda yawanci zuwan da suke yi da biyu suke yi. Domin masu yi mata dariya a bayan fage sun fi yawa saboda irin habaicin da ta dinga yi musu a lokacin da za su tare. Sai daga baya Dada ta shiga a lokacin yawancin mutane sun watse daga Daddy sai su Jafar, Uwani kuwa dama tun da ta shiga gidan ta yi sashen Dada daga nan ta wuce wurin turken awakinta. Sannu a hankali jikin Mami yake ƙara samun sauƙi, ganin yadda Mami ta yi laushi ya sa Uwani ta yi tsammanin ko Mami sauya halinta ne. A haka sai da suka shafe kusan kwana goma a cikin gidan, kuma a wannan kwanakin kullin sai Daddy ya sa an yi saukar karatun Alƙur'ani. Wannan saken da Uwani ta samu ya sa hankalinta ya kwanta, ta manta da matsalar Mami gabaɗaya. Don tun da suka koma Kura sau biyu ta shiga duba Mami, kuma ba wata kyakkyawar fuska take samu ba. Su Mami ba su suka koma gidansu ba sai bai fi saura sati guda bikin Shukra ba, da ƙyar Mami ta yarda ta koma kuma kafin ta koma sai da suka yi musayar ɗaki da Daddy, ita ta koma ɗakin Daddy shi ya koma ɗakinta. A kwalemar fitar da kayan ne aka fitar da Jangwalagwadan da ya shiga ɗakinta, don shi kansa ya galabaita. A lokacin da za su tafi ne Uwani ta saka kuka don cewa ta yi fir ba za ta koma ba, sai da Dada ta lallaɓa ita da Daddy ta amince amma sai cewa ta yi sai dai idan da awakinta za ta koma. Ba musu Daddy ya amince ya ce zai yanki wani wuri a cikin farfajiyar gidan a yi wa awakinta wuri, amma sai bayan bikin su Shukra. Cikin farinciki Uwani ta bi Jafar suka wuce duk da shi ma ba wata fuska take samu a wurinsa ba, amma ba ya zagin ta ko cin zarafin ta. Shirye-shirye sun fara kankama a wurin su Mami da wurin iyayen Salim, da yake Mami na zirga-zirga sai tsangwama da takurar da take yi wa Uwani ta yi sauƙi. Haka kuma Uwani ta fara gogewa da aikin da suke yi da Inna, don wani lokacin ma idan Inna ta gaya mata yadda za ta sarrafa abu ita take yi. Tun ana gobe kamun bikin Shukra hankalin Mami yake a tashe sakamakon wayar da suka yi da mahaifiyar Safna, a kan cewar za su zo ranar Juma'a da safe su tafi ranar Lahadi bayan ɗaurin aure. Sakamakon biyo jirgin da za su yi daga Lagos zuwa Kano. Tun da suka gama wayar gumi yake keto wa Mami. Ganin ta rasa mafita ya sa ta kira Shukra ɗaki. "Shukra ina tsoron asirinmu ya tonu, ina gudun duk plan ɗin da na shirya ya wargatse. Kin san dai matuƙar Safna da mahaifiyarta suka zo gidan ko yaya ne za su iya fuskantar Jafar na da aure, alhalin ni kuma ban sanar da kowa ba bayan Hajiya Falmata." Shiru Shukra ta yi sannan ta ce. "Hanya ɗaya ce, mu nemo abin da zai sa Yaya ya sake ta kawai." "Ta wace hanya kenan?" Shukra ta zuba tagumi tana nazari, da sauri ta dafa Mami ta ce. "Na samo mafita, kin san me za a yi Mami?" Mami ta girgiza kai da sauri. "Sata kawai za mu laƙa mata, ba kin ce Daddy ya ba ki ajiyar wasu kuɗi masu yawa ba? To da su za mu yi amfani." Shukra ta yi ƙasa da murya tana tsara wa Mami yadda za su yi, lokaci ɗaya suka saki dariyar samun mafita. Suna gama tattaunawa Mami ta ɗebo damin kuɗin ta damƙa wa Shukra, Shukra ta ɓoye su a cikin jakarta kai tsaye ta nufi sashen Uwani ita da ƙawarta Fatima. Kuma ko Fatima ba ta san da plan ɗin su Mami ba. Tun da Uwani ta tare sau ɗaya Shukra ta taɓa shiga sai a wannan ranar ta yi na biyu. Shiru ta ji falon babu kowa, sallama ta rangaɗa daga cikin ɗaki ta ji Uwani ta amsa. Ita ma Uwani dawowarta kenan daga sashen Mami don tun da Dada ta zo kusan wuni guda a cen take yi, idan ta dawo ɓangarenta sai dai ko wani uzurin ne ya dawo da ita. Uwani na fitowa Shukra ta ɗan saki fuska tana murmushi ta ce, "Ki je Mami tana kiranki. Sannan kuma ƙawata Fatima za ta yi Sallar Walha, sashenmu hayaniya ta yi yawa shi ya sa na ce ta zo nan." Uwani sakato ta yi tana mamakin yau rana ɗaya da har Shukra ta sakar mata fuska, a sanyaye ta amsa mata sannan ta wuce kiran da aka ce Mami tana yi mata. Uwani na fita Shukra ta faɗa ɗakin Uwani bayan da Fatima ta fita yin alwala, ta janyo drowar madubin ta saka kuɗin a ciki ta mayar ta rufe. Ba su wani jima sosai ba suka fice daga ɗakin bayan Fatima ta idar da Sallah, a ɓangaren Shukra dama kuma buƙatar maje Hajji Sallah tun da buƙatarta ta biya ba ta ga amfanin zaman nasu ba. Uwani na zuwa ta samu Mami a falo ta tsugunna har ƙasa, a lokacin Mami zaune take da matan Baba Mustafa sai ƙawarta Hajiya Falmata. "Uwani ku je ke da Auta ki taimaka mata ku ciro mini wayata ta faɗa bayan gado." Babu musu Uwani ta yi wa Auta magana suka shiga ɗakin Mami, sun sha wahala sosai kafin su samu damar ɗauko wayar tun da can ƙarshen gado ta faɗa. Abu ɗaya ne ya tsaye wa Uwani a rai, a iya sanin ta tun ranar da ta zo gidan Mami ba ta taɓa saka ta aiki tare da Auta ba. Amma sai ta sa a ranta ko don ganin mutane ne ya sa Mami ta yi hakan, don kar a ce har yanzu ba ta ƙaunarta. Wurin sallar Azahar bayan Mami ta yi sallah ta fito falo ta fasa kukan an sace mata maƙudan kuɗin da Daddy ya ba ta ajiya har kimanin raina miliyan biyu da rabi, nan da nan hankulan mazauna gidan ya tashi. Dada na jin haka ta fara sababi rai a ɓace. "A gaskiya ni kam idan aka kwashe kuɗin nan an cuci Mamman, saboda Allah a tara mutane domin harkar arziƙi su ɓige da harkar tsiya? Shi dai ɓarawo bai ji daɗin halinsa ba, ba don sai Hajji zan je Saudiyya ba da babu abin da zai hana na kai ƙarar ɓarawon nan wurin Ubangiji a ɗakin Allah ba." Haka dai kowa da abin da ya dinga faɗa, daga ƙarshe aka ce su waye suka shiga ɗakin Mami a ranar su za a bincika, nan take aka bada shedar Uwani ce da Auta suka ɗauko waya. Kiransu aka yi aka tambaye su kowacce ta ce ba ta ga kuɗi ba, Mami ta bada shawarar a duba ɗakunan kowaccensu, haka aka kasu gida biyu wasu suka yi ɗakin Auta wasu suka wuce ɗakin Uwani. Falonta aka fara dubawa har da ƙasan kujeru, sannan suka wuce ɗakinta, masu duba drower saka kaya na yi, wasu kuma har da leƙa ƙarƙashin gado suke. Kwatsam ana duba drower madubi sai ga kuɗi, nan take mutane suka ɗauki salati. Aka wuce wurin Mami da kuɗi, saboda tashin hankali Uwani jikinta har karkarwa yake yi. Duk yadda Uwani ta so fitar da kanta abin sai ya gagara, ta yi kuka ta yi rantse-rantse babu wanda ya yarda da ita. Hatta Dada a wannan karon ba ta yarda da ita ba, Uwani ta rarrafa gaban Dada tana kuka cikin takaici Dada ta wanke ta da mari sannan ta hankaɗa ta gefe. Daddy ne kaɗai da ya zo ya lallashi ta, a ransa yana wasu-wasin wannan abin da ya faru. Lokacin da Jafar ya dawo ya ji labari ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, nan take kuma Mami ta birkice a kan sai Jafar ya saki Uwani a cewarta ba za ta zauna a ɓata mata tarbiyyar yara ba. Shi kuma Daddy ya sake jaddada wa Jafar umarninsa na ko bayan ransa bai amince ya rabu da Uwani ba. Abin duniya goma da ashirin ne ya haɗe wa Uwani don haka ta koma sashenta, ta faɗa kan gado ban da rusar kuka babu abin da take yi. Lokacin da Jafar ya shiga ya same ta kallon tsana ya wurga mata sannan ya ce. "Wallahi ni dai an gama cutata, a ce wai matata ta rasa wa za ta yi wa sata sai mahaifina, me aka rage ki da shi ci ko sha? Ƙanƙanuwar yarinya da ke ko a ina kika san kuɗi da har za ki sa hannu ki kwashe miliyan biyu da rabi. Ni kam na yi dana-sanin aurenki, ni dai aurenki wallahi bai amfane ni da komai ba sai tsiya. Ya zame mini dole na yi gaggauwar auren Safna, don ba zan zauna ɓacin rai da takaicinki ya kashe ni ba. Shashasha ɓarauniyar banza da wofi." Jafar ya yi tsaki ya fice daga ɗakin. Uwani ta ci kuka kamar babu gobe, tana nan ɗaki Auta ta je ta same ta. "Uwani Allah Ya sani har yanzu ba na jin ke kika ɗauki kuɗin nan, tare fa muka yi komai muka gama." Rai a ɓace Uwani ta ce. "Auta fice mini a ɗaki kada na sauke fushina a kanki." "Don Allah ki saurare ni kada ki yi mana jama'u..." Cikin tsawa Uwani ta katse ta. "Ki fice mini a ɗaki na ce." Auta ta tsorata sosai da yadda ta ga Uwani ta birkice lokaci ɗaya, bayan fitar Auta Uwani ta fara nazarin shigowar Shukra da kiran da Mami ta yi mata. Murmushi ta saki ta share hawayenta a fili ta furta. "Wallahi wannan ƙwallar da na zubar ba za ta tafi a banza ba. Ni Uwani za ku laƙa wa sharri, ai ko kura ta rame ta fi ƙarfin gawurtattun karnuka." Daga haka Uwani ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta, ta koma can sashen su Mami. Yadda mutane ke bin ta da kallo ita ma Uwani sai ta murje idonta ta fara bin su da kallo, hatta Dada fushi take yi da ita don haka ita ma ta yi kamar ba ta san da Dada a wurin ba. Duk in da Uwani ta gifta sai dai ka ji ƙus-ƙus na tashi. Auta ta nema ta ba ta haƙurin abin da ta yi mata, ita ma dama Auta ba ta ga laifin Uwanin ba don idan ita ce ma za ta yi fiye da haka. A cikin dabara Uwani ta tambayi Auta Event ɗin da za a yi kamu, Auta ta nuna mata ai sai su tafi tare tun da ba ta san wurin ba. Yamma liƙi jama'ar gidan ana ta hada-hadar tafiya wurin kamu, Uwani ma atamfarta ta saka da mayafi sai dai tun rana Auta ta hana ta yin wannan ɗige-ɗigen kwalliyar. Ita ta biya musu kuɗin make up aka yi muku kwalliya sai ga Uwani ta fito shar kamar ba ita, lokacin da Uwani ta saka ƙafa a cikin hall ɗin ne ta saki murmushin ƙeta da mugunta. Ta zura hannu cikin aljihun doguwar rigarta ta ji fakitin sabuwar rezar da ta saya tana ciki a fili ta furta. "Uwani ce fa 'yar ƙashin gwiwa, ai yanzu za mu fara wasan da ku tun da haka kuka zaɓa." AlhamduLillah a nan free pages na wannan labarin ya ƙare🫠 idan kina buƙatar ci gaba za ki turo 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar biya ta wannan lamber 07062062624 Sai mun haɗe a shafin gobe idan Allah Ya kai mu domin mu ji tsiyar da Uwani za ta shuka, Fakitin Reza a cikin Hall ɗin kamu na san akwai ƙura.😂 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Baki sake kamar wata sakarya haka Uwani ta saki baki da hanci tana bin hall ɗin da kallo, Auta ce ta ja hannunta jin Mc ya saki kiɗa ta ce. "Uwani mu je mu taka." Girgiza kai Uwani ta yi tana yamutsa fuska ta ce, "Ni fa wani lokacin ba na son yin rawa kawai ki shiga." Wucewa Auta ta yi cikin filin da tsirarin 'yan mata suka fara shiga suna cashewa kafin zuwan amarya. Can kan wata kujera Uwani ta zauna tana bin ƙayatuwar wurin da kallo, tana jinjina irin kuɗin da aka kashe aka yi decoration ɗin gargajiya. Tana nan zaune sai ga Hajiya Mami tare da ƙawayenta sun shigo cikin takun ƙasaita, Mami har wani buɗawa take an sha make up ga wata dakakkiyar jaka a hannunta. Kamar taɓaɓɓiya haka Uwani ta kalli Mami ta fara ɓaɓɓaka dariya, don ma da ƙarar sautin kiɗan wurin da tuni hankulan mutane ya dawo kanta. Zaman Uwani a wurin ya sa ta lura da irin kallon da wasu matan ke yi mata, a fakaice ta lura da yadda wasu ke zunɗenta suna nuna ta a kan maganar kuɗin wurin Daddy da aka gani a ɗakinta. Wani tunani ne ya sake faɗo mata don haka ta miƙe ta fice daga cikin hall ɗin, ta watsar da shirin rezar da ta ci buri yi don ta lura wannan da za ta aiwatar sai ya fi tarwatsa lissafin Mami da Shukra. Waige ta shiga yi hagu da dama sannan ta hango wata 'yar kwana a bayan hall ɗin. Tana cikin tafiya ta hangi wani matashi zaune a jikin bishiya, da alama 'yan zuƙe-zuƙensa yake yi. Uwani ta lura sarai da yadda yake kafe ta da kallo yana murmushi tun kafin ta ƙarasa, tana zuwa daidai wurinsa ta yi masa sallama cikin murmushi ta ce. "Yayana don Allah wani taimako nake nema." Abin ka da me jira da sauri saurayin ya miƙe tsaye yana kaɗe jikinsa ya furta. "Haba 'yan mata faɗi kowanne irin taimako ne an gama shi." Uwani ta ɗan kawar da kai a fakaice, jin tsamin kayan mayen da yake sha ya bugo ta sannan ta ce. "Dama ƙannena ne suke fama da matsanancin tari, to shi ne muke buƙatar jangwalagwada guda biyu za a dafa musu an ce shi ne ƙat wurin maganin tari." Uwani ta yi maganar tana zaro kuɗi daga aljihunta ta ce. "Ga wannan ba yawa don Allah sai a rage..." "Haba ƙanwata, ai aikin lada za mu yi biyar ba zan karɓa daga wurinki ba." Uwani ta yi masa godiya, sannan ya ce mata ta tsaya a nan zai samo mata. Ba a ɗauki lokaci ba sai ga shi ya dawo hannunsa ɗauke da wasu sharɓa-sharɓan ƙadangaru, leda ya zaro a aljinu zai saka mata da sauri Uwani ta ce. "Don Allah idan babu damuwa ka saka mini kowanne daban-daban a leda, don mamanmu ta ce za ta ba wa aminiyarta ɗaya ita ma yaranta tari suke." Matashin ya yi murmushi ya ce, "Ai sai yadda kika ce ranki shi daɗe." Sai da ya saka wa Uwani a cikin leda daban-daban ya miƙa mata, ta ɗauko wani kyallen ragowar atamfarta ta buɗe ta saka a ciki, sannan ta zura a cikin wata ledar suka fara tafiya, suna tafe matashin sai zuba mata hira yake har suka ɗan gota hall ɗin bikin. Uwani ta yi masa dabara ya koma sannan ta koma ta shige cikin hall ɗin. A lokacin da ta je Mami na ta gaisawa da mutane, Auta ta hango zaune a wata kujera da sauri ta zura ƙadangarun cikin aljihun rigarta. "Masu yin rawa an gaji ne?" Uwani ta furta wa Auta tana jan kujerar kusa da ita. Sauke ajiyar zuciya ta yi ta ce, "Ki bari Uwani Mc ne ya kwafsa mana muna cikin rawa ya kashe, wai ba ya buƙatar taron ƙwailaye ki ji iskanci." Uwani ta saka dariya tana shirin magana Mami ta ƙarasa wurin Auta ta miƙa mata jakarta tana faɗin. "Auta riƙe mini jakar nan kafin su Shukra su shigo kin san fa ni dama ba gwanar riƙe jaka ba ce..." Kalamanta suka katse sakamakom ganin Uwani a gefen Auta. "Uban me kike yi a nan? Ɓarauniya nan ma zuwa kika yi kwashi kuɗin jakunkunan mutane? Wallahi ko cokali na ji ana cigiya sai kin yaba wa aya zaƙinta." Mami ta ƙarasa maganar tana wurga mata harara ta bar wurin, wannan ce rana ta farko da Uwani ta ji ta tsangwami kanta ta kuma muzanta. Saboda tsirarun mutanen wurin har sun fara kallonta, idonta ya ciko da ƙwalla Auta ta dafa ta ta ce. "Don Allah kada ki ɓata kwalliyarki Uwani, wai ma Ya Jafar ya gan ki kuwa." Murmushi ne ya suɓuce wa Uwani ta girgiza kai, don ita kanta make up ɗinta ba ƙaramin kyau ya yi mata ba. Auta ta yi ta zolayar Uwani har sai da ta ga ta saki jikinta sannan suka ji an yi shelar za a shigo da amarya da ango. Da sauri Auta ta damƙa wa Uwani Jakar Mami ta nufi bakin ƙofa da yake sune masu anko, sai da suka jajjeru sannan aka saki waƙar Nura M Inuwa ta 'Lokacinki ne ya yi amarya 'yar amana...' Ganin hankulan mutanen wurin ya yi kan Shukra da Salim, wasu na ɗaukan hotuna yayin da wasu ke yin Video ya sa Uwani ta sauke jakar Mami ƙasan table ta ware ƙyallen da ta saka ƙadangaren ta buɗe guda ɗaya, sai da ta zuge jakar ta hango damin kuɗin liƙin da Mami ta tanada. Murmushi ta saki mai sauti sannan ta ɗora jangwalagwadan akan canjin kuɗin, ta wurgar da ledar a gefe ya rage saura ƙadangare ɗaya. Da sauri ta dawo da jakar ta ajiye, ta ci gaba da kalle-kallenta. Babu laifi Shukra ta yi kyau sosai, da yake ta saka atamfa ja da wani yadi mai kalar ruwan toka, shi kuma Salim ya saka dakakken yadi ruwan toka an yi masa aiki da jan zare a babbar rigar. Mami na daga gefe sai sakin murmushi take, a haka har amarya da ango suka wuce kan kujerar da aka tanadar musu. Da zamansu babu jimawa Auta ta je wurin Uwani ta karɓi jakar Mami ta kai mata, daga haka dangin su Salim suka shigo ɗauke da turarukan wuta dana ruwa ana fesawa. Dada ita ma sai a lokacin ta shigo da yake ita Jafar ne ya kawo, ita da wata Kakar Salima suka nufi wurin su Shukra aka ba su turare suka shiga fesa musu. Take wurin ya kacame kowa burinsa ya ga fuskar amarya da ke ƙumshe cikin lulluɓi, Uwani ta zagaya ta bayan kujerar da suke zaune duk yawan mutane ta kutsa daidai kunnen Shukra ta sauya murya ta raɗa mata a kunne. "Muna taya ki murnar amarcewa a matsayinki na 'yar matata. Ki sanar da masoyiyata Saratu zan bata gudunmawar aurenki, kuma kema zan damƙa wa angonki ta ki gudunmawar." Da yake rurumar mutane ta yi yawa babu wanda ya lura da wata Uwani, Uwani na gama magana ta matsa daga wurin tana dariyar ƙeta. Shukra da ke lulluɓe ana buɗe mata fuska har ta haɗa uban gumi sharkaf, gabanta ya shiga faɗuwa tana ɗan waige. A haka aka yi ta hotuna ana fesa musu turare ita da Salim, daga nan kuma MC ya ce su fito cikin fili domin su taka rawa. Ganin sauyin da Salim ya gani tattare da Shukra ya sa ya ɗan yi mata raɗa a kunne. "Dear lafiya kuwa? Na ga kin sauya lokaci ɗaya, saɓanin yadda muka shigo mota." Shukra ta tattaro murmushin yaƙe ta ce. "Wallahi turaren nan ne ya yi mini yawa shi ya sa kaina ya ɗan fara ciwo." Wannan maganar da suke yi ba ƙaramin birge mutane suka yi ba, nan Mc ya ci gaba da wasa su Uwani na daga gefe tana sakin murmushin mugunta. Shigar su Shukra cikin fili ya sa dangin Salim da na Mami suka shiga suka fara yi musu ruwan liƙi, ganin yanayin da Shukra ke ciki ya sa Mami ta zagaya ta yi mata raɗa a kunne. "Haba Shukra ki saki fuskarki mana, kina ga fa duk wanda ya zo wurin nan domin ku ya zo fa." Da sauri Shukra ta zayyana wa Mami duk abin da ta ji a kunneta, tun ba ta gama magana ba Mami ta yi sharkaf da gumi, amma sai ta nuna wa Shukra su basar don su rabu da baƙinsu lafiya, saboda kada a lura da yanayinsu. Ta cikin rurumar rawar da ake yi ne Uwani ta saɗaɗa ta zurawa Salim ƙadangaren a cikin aljihu, ta koma ta gefen Shukra ta raɗa mata cewar. "Mun saka wa angonki gudumuwarki, ki yi gaggawar karɓa yanzu idan ba haka ba mahaifiyarki za mu ɗauke, kuma har abada ba za ku sake ganinta ba." Uwani na gama maganar ta yi sauri ta sulale, hankali tashe Shukra ta fara waige, Mami ganin ƙawayenta da 'yan uwa na ta liƙi ya sa ta zage jaka tana ɗan tattakawa cikin shauƙin rawar da kiɗan da ya ɗebe ta. Ta zura hannu da sauri don ta ɗebo kuɗi ta watsa, a wannan lokacin ne kuma Shukra ta ce wa Salim ya zura hannu a aljihunsa. Bai tambaye ta dalili ba, sai ma ya yi tsammanin ko Shukra na nufin ya yi mata liƙi ne, yana saka hannu a aljihu ya ji abu da laushi har da alamun ƙafafuwa. Yana fito da shi idanun mutane suka sauka a kan nararkeken jagwalagwada, ita ma Mami a wannan lokacin ta fisgo ƙadangaren cikin jakarta da hannunta, da yake da ƙarfi ta ɗauko da niyyar yin liƙi sai kawai gani aka yi ƙadangare ya yi sama. Dada da Kakar Salim wato Inno a guje suka fita daga cikin filin, mutane suka fara guje-guje wasu na faɗa wa ƙasan table. Yayin da irin su Mami suna bazama a guje suna neman maɓoya. Ƙawayen Shukra da ƙannen ango tuni suka bazama, sai ɗankwalaye da mayafai ne suka dinga tashi sama. Uwani da zamanta a ƙarƙashin table ɗin da Dada ta ɓuya kenan, ta dubi Dada da hawaye ya gama wanke mata fuska. Ta tsince ta tana faɗin. "Ni kam Saro ta jangwalo mana masifa, yanzu Allah wannan ƙadangaren ashe bai bar ta ba?" Uwani ta haɗe fuska ta ce. "Kin ci sa a da ba ke ya aura ba?" "Uwarki Maryama kika faɗa wa ba ni ba, almura mai mugun hali wallahi Uwani kin yi asarar halin 'yan ɗauke-ɗauke." Shiru Uwani ta yi wa Dada tana murmushi. Ganin 'yan mata na fita daga hall ɗin a guje ya sa securities ɗin cikin halla ɗin suka shiga suna tambayar abin da ya faru, wasu daga cikin masu ganin ƙwaƙwaf ɗin har sun fara yi wa ƙadangarun vedio suna watsawa a social media. Securites ɗin ne suka kwashe su suka fita da su sannan hall ɗin ya fara dawowa daidai. Sai da komai ya lafa sannan kowa ya fara gane a mahallin da yake, Salim na tsugunne a bayan manyan sifikun Mc sai a lokacin ya farga da ashe akwai mutum a cikin babbar rigarsa. Miƙewa ya fara yunƙurin yi sai a lokacin Mami ta ji yana jan kanta, a tunaninta ƙadangaren ne yake fusgarta. Ihu ta zuba tana jan kanta shi ma Salim ya saki ihu yana jan babbar rigarsa, babu zato sai gani aka yi daga ita har shi sun zube a ƙasa. Da ƙyar Mami ta zaro kanta daga cikin babbar rigar Salim yayin da ɗankwalin gwaggwaronta ta hango shi a saman kan Salim. Cibiri-cibirin gashin Mami duk ya tashi tsaye da bai wuce kamu ɗaiɗai ba, a kunyace Salim ya miƙe yana kaɗe jikinsa sai ji ya yi gwaggwaron Mami ya faɗo. Shukra na daga ƙarƙashin table ta ɗago a hankali tana goge hawayen baƙin ciki, wata ƙanwar Mami ce ta cire mayafinta ta rufa wa Mami a kanta, sannan ta kama ta ta zaunar da ita a kan kujera. Salim neman duniya ya yi wa hularsa bai ganta ba don haka ko ta kan Shukra bai bi ba shi da Abokansa suka fice daga cikin hall ɗin a guje manyan rigunansu sai tashi sama suke yi. Saboda tsananin ɓacin rai sai kawai Mami ta rushe da matsanancin kuka, ita tana yi Shukra na taya ta. Ita kanta Auta jikinta duk ya yi sanyin don abin bai yi daɗi ba. Mami ta sake kallon wurin da irin dukiyar da ta kashe, hatta ɓangaren abinci ta zube masa maƙudan kuɗin abinci. Sai ga shi a cikin hall ɗin ko cokali ɗaya ba ta jin wani ya ci na abinci, ga shi kowa ya tarwatse. Kafin wani lokaci tuni hall ɗin ya ɗaɗe sai tsirarin mutane masu ganin ƙwaƙwaf, lokaci ɗaya ƙananan maganganu suka fara tashi wasu su ce a tsofaffin samarin Shukra ne suka yi mata ture, wasu kuma su ce Salim aka yi wa. A raɗe-raɗin ne maganar auren Mami da ƙandare ta ɓilla, sai da Mami ta ci kukanta ta koshi sannan ta ɗebo takalmanta a hannu sun zo fita sai ga gayyar 'yan jarida sun shigo ɗaukan rahoto. "Sannu Hajiya, a yadda muka fahimta kamar kema wata jigo ce a cikin shagalin auren ko? Shin ko akwai wani ƙarin haske da bayanin da za ki iya yi mana dangane da abin da ya faru?" "Kwatsam Hajiya sai kuma aka riski ƙaton ƙadangare a cikin jakar uwar taro, ko za ki yi tsokaci a kan haka? Shin akwai wanda kuke zargi a kan faruwar wannan al'amarin?" "Hajiya a yadda rahoto ya zo mana an ce sirikin uwar taron ma ya samu tagomashin samun ƙadangare a cikin aljihunsa ko akwai wani abu me alaƙa tsakanin ƙadangaren wurin uwar amaryar da na wurin shi angon?" 'Yan jaridar suka dinga jefa wa Mami tambayoyi, kafe su ta yi da kallo cikin ɓacin rai ta haɗiyi yawu mai ɗaci sannan ya fara sauke fushin ta a kansu tana faɗin, "Da kai, da kai da sauran ma'aikatan gabaɗaya kun ci ubanku. Munafukai masu jiran kaɗan ku ƙara, duk wanda ya ƙara tunkaro ni da tambaya sai na ci ubansa." Mami na gama magana fuuu ta wuce zuciya na suya. Dada da a lokacin ita ma ta samu sukunin fitowa wani ɗan jarida ya tare ta da tambaye. "Hajiya barka da fitowa! Hajiya shin ko akwai abin da za ki faɗa dangane da faruwar wannan abin?" Dada ta riƙe haɓa cikin sanyin jiki sannan ta ce. "Yaro ba dole na samu abin faɗa ba, ni fa na haifi uban Shukra. Ko ba ka san Mammam Mai shanu ba ɗan sanda?" Ɗan jaridar ya sake riƙe abin naɗar muryar cikin jin daɗin haɗin kan Dada da ya samu ya ce, "Hajiya waye bai san Mai shanu ba ai fitacccen ɗan sanda ne." "To mu dai muna tsaye mun gama kama amarya da ango sai Saro ta saka hannu a jaka sai fa kawai ƙadangare muka gani, kai na yi mantuwa shi dai ƙadangaren kwanakin baya ya tarfa Saro a bayi tana wanka wai ya aure ta. Ni dai ban san me ya kawo shi yau ba, ina kira ga malaman garin nan su kawo wa Mamman ɗauki kada sabon angon Saro ya halaka mini ɗa." Dada na gama faɗar har ta yi gaba sai kuma ta sake dawowa. Wani ɗan jaridar ne ya sake tunkararta ta dakatar da shi sannan ta tara duka sauran 'yan jaridar, sai da kowannensu ya gama saita na'urar ɗaukar sautinsa sai kawai Dada ta fashe da kuka. Ganin kukan Dada ba mai ƙarewa ba ne ya sa suka fara kashe na'urar naɗar sautin suka shiga rarrashinta, ta share hawaye da gefen mayafinta sannan ta ce. "Kaicon wannan lusari da zai tsaya yana bibiyar Saro da zuri'arta domin abin da ya yi Mamman shi ya yi Saratu. Yaro shekararsu sama da talatin da biyar da aure, shin Saro ba ta zama Mamman ba?" Dada ta tambaye su, cikin haɗain baki suka amsa mata ta ci gaba da cewa. "Ai ni tsohuwa ya kamata wannan ƙadangaren ya tunkara domin mune muke kan hanyar tafiya, ba Saro da ke fama da ɗawainiyar Mamman da iyalansa ba." 'Yan jaridar suka shiga kallon-kallo kowa da abin da yake raya wa a ransa, wasu kuma sai murmushi suke. Dada ta dunƙule hannuwa, sannan ta ɗaga su sama jikinta har karkarwa yake cike da rashin tsoro ta ci gaba. "Ni na sadaukar musu da kaina amma su ƙyale iyalan Mamman su zauna lafiya..." Atika 'yar wurin Dada ta biyun ƙarshe ta ɗan zunguro Dada tana ƙasa da murya ta ce. "A'a Dada su fa mutanen nan ba a yi musu haka!" Dada ta doke hannun Atika a ɗan fusace ta sake mayar da kallonta wurin 'yan Jaridar ta ce. "Ina kira da babbar murya, duk wani taƙadirin aljani a shirye nake da ya tunkaro ni. Ni Kulu yadda su Mamman suka faranta mini rai ba zan bari a tarwatse zaman lafiyarsu ba. Ni na bar ku lafiya na gode kowa zai iya tafiya." Dada na gama magana hayaniya ta kacame a wurin, Uwani da ke gefe ta zuba wa Dada ido a ranta ta furta. "Za ki yi mini bayani kuwa." "Hajiya ko akwai abin da kika taka da har kike irin wannan iƙirarin?" Wani ɗan jarida ya tambayi Dada. Ta waiga ta ce. "Kai yaro wannan yaƙin da kake gani na zuri'ata ne zan iya tarar komai da kowa a kansu." Daga haka Dada ta fice. Duk yadda suka so sake jin ta bakin Dada ba ta kula su ba, a haka kowa ya watse. Lokacin da kowa ya koma gida haka aka haɗu aka dinga jajantawa, abincin da Mami take ta kaffa-kaffa da shi da kajin ciki tana ji tana gani aka baje shi da daddare aka cinye. Shukra kuwa tun da ta shiga ɗakinsu ban da kuka babu abin da take yi. Cikin Dare Cikin sanɗa Uwani ta fice daga sashenta don lokacin bacci Jafar yake har da munshari, kasancewar a ranar suka dawo daga kaduna shi da Ibrahim a kan wani aike da Daddy ya yi musu don su wakilce shi, ya sa ya gaji tuɓus. Kamar mara gaskiya haka ta dunfari sashen Mami, ta yi sa'a kuma a buɗe yake don haka tana shiga ta leƙa ɗakin da su Dada suke ciki. Shi ma a buɗe ta same shi duk sun baje sai sauke munshari suke yi, kashe glub ɗin falon ta yi ta ciro wata wayar caja ta riƙe. Da Sajida ta fara cin karo matashiyar budurwa ce 'yar wurin Baba Inusa, sai da Uwani ta ja wata ƙatuwar hular sanyinta ta rufe fuskarta ta fara jan hannun Sajida, sai da kawo ta falo sannan ta ɗaga wayar caja ta zuba mata a baya. A zabure Sajida ta miƙe tana susa ta shige ɗakin a guje, Uwani ta saki murmushi lokacin da ta reƙa hannuwan Dada ta fara ja. Dama saboda yanayin cinkoso da zafi Dada daga ita sai ɗaurin ƙirji. Tun da Uwani ta fara jan Dada zanin jikinta ya faɗi daga ita sai ɗan tofi, cikin bacci Dada ta ji ana janta tana buɗe ido ta ganta a duhu. "Waye haka yake figa ta cikin dare kamar kaza?" Dada ta faɗa a tsorace. Uwani ta kausashe murya ta ce. "Mune da kika gayyato kika ce za ki yi yaƙi da mu, ga mu mun zo tafiya da ke mu kacalcala namanki." Uwani na faɗar haka ta saka hannu ta fisgo maman Dada ta ci gaba da cewa. "Da farko dai za mu saka lauje mu yanke waɗannan abubuwan, sai mu feɗe su mu yi banda ranar amarcin sabuwar matar da za mu aura mu ci amarci da su, tun da kina yunƙurin hana mu keɓewa da Saratu." Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar biya ta wnn lambar 07062062624 idan littafi ya kammala cmplt 800 #Ummou Aslam Bint Adam *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Dada na jin abin da Uwani ta faɗa da sauri ta saka hannuwa biyu ta dafe ƙirjinta tana faɗin, "Ku dubi girman Allah kada ku yi banda da ni." Uwani ta sake cukwikwiyo ƙirjin Dada ta ce, "Mu ai ba da ke za mu yi banda ba, yanke waɗannan za mu yi. Kai ku ba ni laujen nan na girbe tsohuwar nan." Dada na jin haka ta rushe da kuka, dama tuni futsari ta gama jiƙe ɗan tofinta. Duk da a cikin duhu ne ba ta ganin Uwani amma sai ta haɗa hannuwa biyu alamar roƙo ta ce, "Don Allah ku taimaka ku yi mini rai." Uwani ta yi wani gurnani ta dafa Dada tana wata irin girgiza ta furta, "Za mu rabu da ke, amma zan kira yanzu ɗan autan kwaratan cikinmu sai ya miki fyaɗe don na ga ke taurin kai gare ki." Tun Uwani ba ta gama magana ba Dada ta sake rushe wa da kuka tana faɗin. "Yau kam ni nake ganin rayuwa, ni Kulu yau ni ce kwarton aljani zai wa fyaɗe wayyo jama'a ku kawo nini ɗauki." Jin Uwani ta yi shiru ya sa Dada ta fara rarrafawa, sai da Uwani ta bari Dada ta kusa kai wa ɗaki ta sa hannu ta sake zugo ƙafafuwanta. Uwani tana cikiniyar sake riƙo ƙirjin Dada sai kawai Dada ta yi kukan kura har da wani zillo ta doke Uwani gefe ta faɗa ƙofar a guje ta shige ciki, Uwani saboda tsabar dariyar da take yi ƙasa-ƙasa har sai da ta kwanta. Ba ƙaramin mamakin ƙarfin Dada da gudun ta Uwani ta yi ba, a iya sanin ta Dada ko tafiya take tana ɗan ɗingisawa amma yau wuya ta sa ta ware ƙafa ta zuba a guje. Duk budurin da ake yi wasu daga cikin mutanen ɗakin bacci suke yi, Uwani ta suri wayar cazar ta shiga ɗakin su Dada waɗanda suke kwance ta shiga fyauɗa musu, lokaci ɗaya ɗakin ya kaure da ihu da koke-koke. Gudun kada asirinta ya tonu ya sa ta yi saurin ficewa daga ɗakin. Da sauri ta laɓe a kusurwar bango ganin Daddy ya taho da sauri hankali a tashe, sai da ta ga Daddy ya wuce ta yi sauri ta wuce ta nufi sashenta. Daddy na shiga ɗakin ya kunna fitilar ɗakin, a tsaye ya hangi Dada daga ita sai ɗan tofi ta ɗauki akwatin kaya ta ɗora a kanta. Fuskarta sharkaf da hawaye, ga wani irin fitsari da take saki lokaci-lokaci saboda tashin hankali. "Dada lafiya kuwa? Mene ne yake faruwa?" Dada na jin haka ta sake rushewa da kuka tana faɗin. "Ni dai Mamman ka zo ka kai ni kura." Da mamaki ya zaro ido waje ya ce. "Kura fa Dada? A tsohon daren nan?" Dada ta gyaɗa kai ta ce. "Wallahi ganin idona yau har autan kwaratan waɗancen jinsin na gani, ni dai ba zan ambaci sunansu ba ballantana su ce da su nake. Don Allah Mamman dube ni tsofai-tsofai za a yi wa fyaɗe, tun daga ƙuruciya ban ga wannan iftila'in ba sai yanzu da komai ta saki kamar robar wando." Dada na zuwa nan ta sunkuyar da kai ta kalli ƙirjinta ta cikin kuka ta ci gaba da magana. "Ba don Allah ya dubi tsufana ba Mamma da tuni har 'yan mazauna ƙirjina za su tsintsinke, ni dai wallahi duk furucin da na yi jiya a wurin 'yan Jarida aikin sheɗan ne." Daddy ya sauke wa Dada akwatin kanta sannan ya furta. "Dada har yanzu fa ban fahimci me yake faruwa ba." Sai da Dada ta share hawayenta sannan ta kwashe duk abin da ya faru ta faɗa masa, shiru Daddy ya yi abin duniya goma da ashirin ya mamaye shi. Ya mayar da kallonsa wurin ragowar mutanen ɗakin da ke tsaitsaye suna susar wurin da Uwani ta shauɗa musu wayar caja. "Dada yanzu don Allah ku yi haƙuri zuwa safiya, In shaa Allah zan san abin yi." Dada ba ta amsa ba sai sauran mutanen ɗakin ne suka amsa, Daddy har ya juya zai fita da sauri Dada ta riƙo hannunsa. "Wallahi Mamman ƙafata ƙafarka, mu je can ɗakinka har zuwa wayewar gari." Daddy bai musa ba ya jira Dada ta janyo doguwar rigarta ta shiga banɗaki ta wanke jikinta, ta saka rigar sannan suka fice daga ɗakin. Koda suka je can ɗakinsa a kan katifarsa Dada ta kwanta, tun tana gyangyaɗi har dai bacci ya yi awon gaba da ita. Hannuwa biyu Daddy zuba yana tagumi saboda abubuwan da suke faruwa, mamakinsa bai wuce duk malaman da yake kira su yi karatu ba nuna masa suke gidan lafiya ƙalau yake babu wasu sheɗanu da ke ciki masu tayar da hankali. Mayar da kallonsa ya yi wurin Dada da ke ta sauke munshari, ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ɗauro alwala ya tayar da sallar nafila. A ɓangaren Mami ma ta jima bacci bai ɗauke ba sakamakon tunani da ɓacin ran da ya mamaye ta, sai da su Hajiya Falmata suka dinga lallaɓarta suna kwantar mata da hankali. "Ƙawata wannan lamarin yana ɗaure mini kai, ni kam ban san jarrabawar da ta same ni ba. Yanzu babban tashin hankalina lokacin Dinner kada shi ma a sake hargitsa mini mutane." Mami ta furta ƙwalla na zuba, Hajiya Falmata ta furta. "In shaa Allah hakan ba zai faru ba, sai mu sa a yi addu gari na wayewa." Sun jima sosai suna ba wa Mami baki sannan ta ɗan saki jikinta. Koda asuba ta yi Dada a ɗakin Daddy ta yi sallar, bayan Daddy ya dawo daga sallar asuba da suka gama gaisawa da Dadda ya ɗauki wayarsa kamar da wasa ya shiga Facebook. Gidan wata jarida ya ga sun wallafa rubutun da ya ja hankalinsa mai taken: 'Tattaunawa da mahaifiyar Babban ɗan sandan nan DC Muhammad Mai shanu kan abin da ya faru a wurin taron bikin 'yarsa Shukra.' Da sauri Daddy ya yi linking ga mamakinsa sai ga Vedio Dada raɗau tana jawabin da 'yan Jarida suka ɗauka. Dada na jin sautin muryarta tana gefe ta rushe da kuka ta ce, "Mamman don Allah ka taimake ni ka sa 'yan jaridar nan su goge wannan jawabin nawa, wallahi ko su goge ko kuma duka ka yi ƙararsu." Daddy ya yi kasaƙe yana ci gaba da kallon Video Dada ba tare da ya tanka ba har sai da ya gama sannan ya ce. "Dada ai aikin gama ya gama, da kanki fa kika ce su ɗani sautunki ga shi wasu har da vedio sun ɗauka. Ashe dama ke ce kika gayyato mutanen da suka tarfa ki da kanki?" Dada ta sake yi tsilli-tsill da idanu tana hawaye, Daddy ya sauke ajiyar zuciya rai a ɓace ya furta. "Allah Ya kyauta." Yana kashe data ya fara cin karo da sakwanni a wayarsa na gidajen manyan Jaridu suna gayyatar a yi hira da shi a game da video Dada. Babu wanda ya yi wa replay, kuma kafin wani lokacin tuni vedio Dada ya zaga social media gabaɗaya, da yawan mutane sai suka mayar da shi abin barkwanci musamman da labarin abin da ya faru da Dada da dare ya ɗan fara ɓulla waje. Bayan da gari ya waye Mami ta zo gaishe da Daddy bayan sun gaisa ya sa ta kira masa Shukra, fuskarta ta kumbura suntum saboda kukan da ta sha. Sai bayan da ta gaishe shi sannan ya ce. "Shukra duk abin da ya faru na ji labari har kawo abin da ya faru a cikin gidan nan da daddare. Mun yi kuma waya da Malam Idi mai Baƙara zai zo shi da ɗalibansa a yi karatu a gidan nan." Mami da Shukra suka gyaɗa kai sannan Daddy ya ci gaba. "Sannan abu na gaba da nake son sanar da ke idan har akwai wani kiɗe-kiɗe da kuke shirin yi ku haƙura da shi, domin duk waɗannan abubuwan na sake janyo sheɗanu..." "Daddy yau fa za mu yi Dinne kuma duk mun sanar da ƙawayenmu shi ma Salim ya gayyato abokansa..." Shukra ta katse Daddy cikin kuka. Ƙuri ya yi yana kallonta sannan ya ce. "Shukra hanyar lafiya a bita da shekara, ki duba ki ga irin abin kunyar da aka ba ni labari ya faru a wurin taron na jiya, yanzu kun fi son ku yi abin da duniya za ta yi yawo da ku?" "A gaskiya Daddyn yara ba ƙaramin kuɗi fa yaron nan ya kashe ba, yanzu don ƙaranta sai kawai a ce an fasa. Wallahi tsaf mutane za su ce dama can ƙarya muke ba a kama hall ɗin ba." Murmushin takaici Daddy ya yi sannan ya furta. "Lallai Saratu da alama har yanzu ba ki gama shiga taitayinki ba, amma tun da haka kika zaɓa ga fili ga mai doki." Shiru Mami da Shukra suka yi sannan ya ce, "Na gama za ku iya tafiya." Babu musu kuwa Shukra da Mami suka fita, suna fita Shukra ta ja hannun Mami ta furta. "Mami shi ma fa Salim ya gama tsorata don ya ce bazai je Dinner ba." Mami ta hangame baki jiki a sanyaye ta ce, "To yanzu me za mu ce wa mutane Shukra? Ke fa mace ce ke ba ki san kissar da za ki yi ki shawo kansa ba. Haba Shukra kina ga fa yanzu haka jirginsu Safna ya kusa sauka, yanzu ƙawayena me zan gaya musu?" Shukra ta share ƙwalla ta ce. "Shi kenan zan sake tuntuɓarsa na ji." Mami ta ci gaba da ɗora Shukra a kan abin da ya dace ta yi don ta shawo kan Salim. Kusan ƙarfe goma na safe Jafar ya fito daga wanka yana tsaya a gaban mudubi yana taje kansa, wasu sababbin riga da wando ya fito da su kusan kala uku. Sai da ya zaɓi wacce ta fi kyau a ciki sannan ya saka, ya sake tsaya wa a gaban mudubi yana ƙare wa kansa kallo. Shigar Uwani ɗakin kenan ta bi shi da kallo ganin irin gayun da ya sha, rana ta farko kenan da ta ga Jafar ya yi masifar yi mata kyau. Lumshe idanu ta yi jin yadda take shaƙar ƙamshin turarensa, ta sake ware idanunta a kansa tana faɗin. "Wai dama haka kake da kyau Ya Jafar ban sani ba, wallahi ba ka taɓa yin gayu irin na yau ba." Jafar na jin haka ɗan tsuke fuska, Uwani ta taɓe baki ta furta. "Kai fa dama matsalata da kai baƙin hali, ina laifi don an yabe ka. Amma kai komai a ƙunci yake a wurinka, shi ya sa kullin fuskarka kamar fate..." Uwani ba ta gama magana ba Jafar ya fusgi hannunta ya zaunar da ita a gefen gado, ya ɗora ƙafarsa a gefenta fuska a haɗe ya ce. "Rashin kunya za ki yi mini?" Uwani ta murguɗa baki tana ɗauke kai gefe. Kunnenta ya riƙo da hannunsa ya murɗe da ƙarfi kamar zai tsinke mata su, ƙara ta ƙwalla tana runtse ido. Jafar ya sake haɗe fuska sannan ya fara magana. "Ki nutsu ki saurari abin da zan gaya miki!" Ganin yadda Jafar ya birkice mata lokaci ɗaya ya sa Uwani ta shiga taitayinta, riƙon kunnen da ya yi mata ya sa ta shiga haɗa gumi saboda azaba. "Yau su Safna za su zo gidan nan, wallahi-wallahi ko da wasa na kuskura na ga kin nuna wata alaƙa a tsakanina da ke sai na karairaya ki. Ke daga yau kin ji na rantse miki matuƙar kika sake nuna wa wani ma ni mijinki ne wallahi sai na bi dare na fita da ke daga gidan nan, na kai ki can dokar daji na harbe ki na wurgar da gawarki." Tuni cikin Uwani ya kaɗa jin an ambaci bindiga, a tsawace Jafar ya furta. "Ba za ki amsa mini ba?" Da sauri Uwani ta hau gyaɗa kai tana hawaye, ganin yadda ta tsora ta ya sa Jafar ya ci gaba da cewa. "Ko sunana na ji kin ambata sai na saka bakin bindiga na harbe ki, hanyar jirgi daban ta mota daban don haka ki kama kanki, zama da ke na ɗan lokaci ne don ina shawo kan Dada da Daddy zan sallame ki. Safna ita ce zaɓina ita nake so zan aura saboda ita ce daidai da class ɗina, kin ji me na gaya miki ko?" Uwani cikin kuka ta amsa masa. Sai da Jafar ya gama tsurar da Uwani sannan ya ta shi ya fice daga ɗakin. Zuciyar Uwanu ban da zafi babu abin da take yi, ita kanta ba za ta ce ga dalilin jin zafin zuciyar ba. Amma abin da ya fi tsaye mata a rai wai Safna ita yake so yake ƙauna, ƙwafa ta yi ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta ta koma kan gado ta yi lamo ranta duk babu daɗi. Jafar na fita kiran Mami ya shigo wayarsa sai da ya shiga motarsa sannan ya ɗauka, "Mami..." "Wai Jafar me kake yi da ba za je ɗauko su Hajiya ba?" Mami ta katse shi da sauri. "Mami kin gan ni a mota yanzu haka fita zan yi." Mami ta saki murmushi ta ce. "Ka yi sauri don kada su yi ta jira jirginsu yanzu haka ya kusa sauka." Jafar ya ba ta amsa har zai katse kiran ta ce, "Maza kuma ka turo mini Uwani ɗakina ka ce ina son ganinta yanzun nan." Bayan Jafar ya amsa ya fice daga motar ya koma wurin Uwani, Uwani na ganinsa ta kawar da kai. Shi ma bai kalli inda take ba ya ce. "Mami na son ganinki a sashen ta yanzun nan." Yana gama maganar ya fice. Jiki babu ƙwari Uwani ta wuce sashen Mami a falo ta same ta, tana zuwa Shukra ta ja hannunta suka shiga ɗakin Mami. Mami ta bi su a baya tana wurga wa Uwani harara, Uwani na tafe gabanta na faɗuwa har suka shiga ɗakin. "Don uwarki kiranki na yi in yi miki kashedi, yanzu haka matar da Jafar zai aura ita da mahaifiyarta suna hanya. Wallahi ko da wasa na ga kin yi wani alamu ko kin faɗa wa wani alaƙarki da Jafar idan na riƙe ki sai na kusa kashe ki, kin san dai abin da ya faru a kan kuɗin Daddy da na sa Shukra ta kai ɗakinki ta ɓoye aka gansu a wurinki ko? Wallahi a wannan karon kika ɓata mini bajat sai na laƙa miki sharrin da za a ɗaure ki har ƙarshen rayuwarki, kin san zan iya aikata fiye da haka ko?" Da sauri Uwani ta gyaɗa kai tana hawaye, Shukra ta zuba mara ranƙwashi a kai ta ce. "Shegiya baƙa mai baƙar aniya, tun da kika zo gidan nan muke ta haɗuwa da masifa jaka mai ƙashin tsiya..." Shukra ba ta gama magana ba suka ji an turo ƙafar ɗakin da ƙarfi, Dada ta fasa kuka tana faɗin. "Ke dai Saro kin yi asara wallahi, ashe sharri kika laƙa wa Uwani muka dinga aibanta yarinyar nan? Wallahi dama tun da na hango ku ke da Shukra kun janyo ta ɗaki haka kawai na ji ban yarda da ku ba, Saro tun wuri ki nemi yafiyar yarinyar nan domin kin ɗauki haƙƙinta."Mami da Shukra lokaci ɗaya suka rikice, Mami ta saki murmushin makirci da ta yi wani tunani ta ce. "Yanzu Dada ƙiyayyar da kike yi mini har ta kai ki yi mini sharri, idan na yi wa Uwani sharri wacce riba zan ci." Dada na shirin yin magana suka ji an sheƙa ruwa a banɗaki, wani abu ya sake tsarga wa Mami tana fargabar wanda ke cikin banɗakinta ba tare da ta sani ba. Daddy ne ta turo ƙofar banɗakin ya furta. "Ribar abin duniyar da kike son cim ma! Wallahi tun ranar da abin ya faru na ji a jikina Uwani ba za ta taɓa ɗaukan maƙudan kuɗi har sama da miliyan biyu ta kai ɗakinta ba, kin kyauta Saratu wallahi ko iya taron ki da ya wargaje miki a gaban mutane jiya ya ishe ki ishara. Haƙƙin ɗan adam abin tsoro ne amma saboda kin tsani yarinya har za ki laƙa mata sata." Mami da Shukra suka yi zuru-zuru, Dada ta share hawayen idonta ta ce. "Wallahi ni kam Saratu tsoro take ba ni kuma tsaf za ta iya kashe mini Uwani, don haka idan na tashi tafiya ƙafata ƙafarta. Jafaru ko shi ne ɗan autan maza Uwani ta gama aurensa." Dada na gama magana ta ja hannun Uwani suka fice daga ɗakin. A sanyaye Mami ta dubi Daddy ta furta, "Daddyn yara..." A zafafe ya ɗaga mata hannu ya katse ta. "Ba na son jin komai daga gare ki Saratu, duk irin ƙiyayyar da na san kina yi wa yarinyar nan ban taɓa tsammanin ta kai haka. Duk fa a kan Safna kike aikata haka ko? Jafar dai ɗana ne kuma duk duniya babu mai iko shi sama da ni, wallahi-wallahi kin ji na rantse idan ban ga dama ba Jafar ba zai auri Safna ba. Tun da na mallaki hankalin kaina Dada ba ta taɓa ba ni umarni na tsallake ba, amma a wannan karon ko mahaifiyata ba za ta saka ni abin da ban yi niyya ba. Mu zuba ni da ke mu gani idan har tusa na hura wuta." Daddy na gama maganar ya fice a fusace. Daga Mami har Shukra rasa mai bakin magana aka yi, wannan shi ne tashin hankalin da ba a saka masa rana. Lokaci ɗaya Mami ta fara hawaye, wata irin nadama ta ɗarsar mata don ta tabbata a wannan karon ta kai Daddy maƙurar bango. "Mami ki daina kuka don Allah, ba na son wani ya fahimci abin da ake ciki. Kin san fa mutane ba sa raina abin magana." Goge hawaye Mami ta yi abin duniya goma da ashirin ya haɗe mata. Dada na shiga ɗakinta ta rushe da kuka, nan mutane suka shiga tambayar ba'asi. Tiryan-tiryan Dada ta ba su labarin abin da ya faru, lokaci ɗaya suka ɗauki salati kowa da irin abin da faɗa akan Mami. Lokacin da Jafar ya isa airport jirgin su Safna tuni ya sauka, kiranta ne ya shigo wayarsa bayan ya ɗaga ya kwatanta mata a wurin da yake. Babu jimawa sai ga Safna ita da Momma sun ƙaraso, kowacce hannunta ɗauke da jaka. Safna sanye take da doguwar rigar abaya, ba ta yi wata kwalliya ba don dama ita tarkacen kwalliya bai dame ta. Har ƙasa ya tsugunna ya gaida Momma sannan ya karɓi jakarta, Safna sai wurga masa kallo take cikin shauƙin so da ƙauna. Ba ƙaramin kyau ya yi mata ba, bayan Momma ta shiga mota ta gagara haƙuri ta ce. "Baby ka yi kyau, na ga har wata ƙiba ka yi me ye sirrin?" Ta ƙarasa maganar rana kashe masa ido ɗaya, murmushi ya yi mata yana mata alamun da Momma na mota don haka ya yi saurin shige wa mota ita ma ta buɗe ta shiga tana sakin murmushi. Lokacin da suka ƙarasa gida Daddy yana gate yana zirga-zirga, Jafar na yin parking ɗin mota bayan da su Momma suka fito ya ƙwala masa kira. Jafar na zuwa wurin Daddy rai a ɓace ya furta. "A yanzu ba sai anjima ba, ka sanar da mahaifiyar budurwarka ina son ganin ta. Kuma ina son ka shafe duk wani babin soyayyar da kake yi wa Safna daga zuciyarka." 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Jin kalaman Daddy ya yi daidai da jin mummunar faɗuwar gaban da ta mamaye shi ba tare da ya yi tsammani ba, lokaci ɗaya jikinsa ya ɗauki karkarwa idanunsa suka yi jawur. Hannu ya sa ya dafa bango yana jin wata irin juya na ɗibansa, wani irin gumi ne ya shiga keto masa da ƙyar ya samu sukunun kallon mahaifinsa ya furta. "Daddy me yake faruwa!" "Sai wani abu ya faru? Umarni ne kawai na ba ka..." "Don Allah Daddy idan wani laifin na yi maka ka gaya mini don na gyara kuskurena." Daddy ya kafe Jafar da kallo yana nazartarsa sannan ya ce. "Babu wani abin da ka yi mini, ka je kawai zan yi nazari a kai." Daddy na gama magana ya shige ta ƙofar baya. Tun bayan da Daddy ya kira Jafar su Momma suka fito daga mota Shukra ta fito ta tafi da su, can sashen Mami ta kai su aka shiga tarbarsu cikin mutumci da karramawa. Mami sai yaƙe take don kar a fahimci halin da take ci, nan suka baje aka shiga hira Hajiyan Safna na yi mata Allah sanya alheri da kuma jajen abin da ya faru ranar kamu. Jafar na ganin Daddy ya tafi kai tsaye sashensa ya koma don a tsammaninsa wani abin Uwani ta samu Daddy ta gaya masa, ganin ba ta nan ya sa ya saki ƙwafa rai ɓace ya kwanta a kan kujera yana jin ƙirjinsa na zafi. Wata irin tsanar Uwani ta tsargar masa yana ayyana irin hukuncin da zai yi mata idan ta shiga hannunsa. Yanan nan zaune ya ji kiran Safna ya shigo wayarsa, sai da ya ɗan saita nutsuwarsa sannan ya ɗaga. "Baby ina ka tafi ne." Jafar ya saki murmushin yaƙe ya ce. "Daddy ne ya saka ni wani aikin amma na gama ki fito gate mana, kin san ciki mutane sun yi yawa." Amsa masa Safna ta yi sannan ya katse wayarsa ya fice. A ɗan zagayayyan wurin hutawa mai ɗauke da kujeru suka zauna, Safna ta kalli Jafar cike da so ta ce. "Hubby kamar ba ka yi missing ɗina ba, duk na ganka wani some how." Jafar ya saki murmushi ya ce, "Burin zuciya da ruhina mallakar farincikin da koda ina cikin baƙin ciki tunaninta na yaye mini shi. Kin kasance walƙiyar da ke haske birnin zuciyata, kallon fuskarki na mantar da ni wanzuwar hallitar kowacce 'ya mace a doron ƙasa. Lafazinki na ratsa mini lungu da saƙon majiyar sautina, tamkar busar sarewar da ke nishaɗantar da me sauraro. Tsayawa surutanta siffa da tsarin hallitarki tamkar giɓi ne ko wata iyaka da zan yi miki domin kyawunki ya zarce tunanin mai tunani. Mallakarki shi ne babban buri da muradin raina a duk bugun numfashin da ke fita daga ruhina, rashinki a kusa da ni kan jefa ni a tekun damuwar da jin muryarki ne kaɗai ke iya yi mini zabarin da zan iya fitowa daga ciki. Ina ƙaunarki Cutie, ƙaunar da ba zan iya fasaltata ba har ƙashen rayuwata." Jafar ya ƙarasa maganar yana sakar mata murmushi, hannu ta sa ta rufe fuskarta. Suka ci gaba da hirar soyayya, lokaci ɗaya Jafar ya nemi damuwar da yake ciki ya rasa. Uwani ganin asirin Mami ya tonu ya sa ta shiga yi wa Dada shagwaɓa son ranta, jin Dada ta sake maimaita maganar tafiya gida da ita ya sa Uwani ta zumɓuru baki gaba ta ce. "Dada ni fa gaskiya ba zan bi ki ba, sharri ne dai Mami ta yi mini ni dai na yafe mata. Nan fa Dada na haɗa shayi da kaina na saka madara son raina, wallahi ko kallon banza Ya Jafar ba ya mini. Ke kuwa idan na haɗa shayi kin dinga mitar zan shanye miki kayan shayi, gaskiya nan na fi cin daɗi. Ga alkakina da dublan nan kullin sai na ci, sugan ma da biredi nake ci. Wai Dada ba ki ga na yi ƙiba ba?" Dada ta yi ƙwafa cikin jin haushin Uwani ta ce, "Sakaryar ba a ƙaunarki a wuri kina manne sai ki yi ta zama ai." Uwani ko a jikinta ta kwanta a cinyar Dada. Abin da ta saka wa ranta za ta ci gaba da zama a gidan Mami tana karta mata rashin mutimci, ita ma tana karta mata nata. Wuni guda Jafar da Safna tare suka yi da juna, bayan la'asar ya ɗauke ta a mota suka dinga zaga gari. Shi ne saya mata wannan saya mata wannan, har sai gabanin magriba suka dawo gida. A wannan lokacin ne kuma 'yan matan gidan suka fara shirin tafiya Dinner, Shukra ce ta kira Safna ta ce mata ta shirya za su tafi wurin make up. Jafar ya ce su tafi shi da kansa zai ɗauke ta ya kai ta, idan an gama yi mata kwalliya ya ɗauke ta su wuce hall ɗin tare. A wannan karon ma Uwani ita da Auta tare suka tafi wurin kwalliya, Auta da kanta ta shiga ɗakin Uwani ta zaɓo mata kayan da za ta saka. Wani dakakken leshi ta ɗauko mata sky blue da ratsin adon ja, an yi mata ɗinki doguwar rigar bubu. Make up ɗin da aka yi wa Uwani ba ƙaramin kyau ya yi mata ba, saboda hodar da aka yi mata amfani da ita duk kalar fatarta ce. A wannn karon da ta kalli kanta a mudubu bayan an yi mata ɗaurin ɗankwali ba ƙaramin kyau ta ga ta yi ba, bayan an gama yi wa Auta kwalliya suka wuce a lokacin ƙarfe takwas na dare ta yi. A can gidan Mami kuwa tun da Dada ta ga an fara shiryawa za a tafi wurin Dinner Dada ta ce Allah Ya kashe ta ba za ta ba, don ta ce babu yadda za a yi ta sake zuwa sheɗanu su dinga kawo farmaki. Daddy ma yana barandarsa yana ganin duk wainar da ake toyawa, a rasa yana mamakin hali irin na Mami. Hall ɗin ba ƙaramin kyau ya yi ba, Shukra ita da Salim aka sauke a bakin hall ɗin. Ƙawayen shukra da suka yi anko ne suka fita a jere cikin birgewa, wani narkakken material Shukra ta saka an yi mata ɗinkin amare irin gown ɗin nan wanda yake ja daga baya. Uwani na zaune sai raba idanu take don a wannan karon hall ɗin ba ƙaramin tashin kanta ya yi ba, har a ranta tana wasu-wasin ko za ta iya aiwatar da ƙudurin da ta zo da shi. Tana nan zaune su Shukra suka shigo gwanin birgewa, take kallo ya koma kansu don kowa ya yaba da tsarin shigar da suka yi daga amare, ƙawayen amare har abokan ango. Mami zaune take a kujera ita da su Hajiyan Safna, kallo ɗaya za ka yi wa tufafin jikinsu ka san an narka dukiya a wurin. Musamman Mami da ta saka wani ɗanyen leshe mai walwali da ɗaukan ido, ta sha kwalliya ɗaurin nan ya yi dass tamkar ba ta ajiya su Jafar ba. Shigar su Shukra babu wuya Uwani ta miƙe za ta fita waje, don ta samu ta ga tsarin wurin ta yadda take so ta samu damar baza manufarta, saboda ta ci alwashin sai ta ƙunsa wa Mami baƙincikin da zai kafa mata tarihi a kundin rayuwarta. Tashin da za ta yi idonta ya sauka a kan Jafar da ke zauna a wata kujera shi da Safna, lokaci ɗaya ƙirjin Uwani ya buga don ko ba a faɗa mata ba tabbata ta kusa da Jafar ce Safna, duba da yadda suke sakarwa juna murmushi suna hira cikin so da ƙauna. Ƙwalla ce ta ciko mata ido ba tare da ta san dalilinta ba, ta haɗiyi yawu mai ɗaci. Tana shirin fita suka haɗa ido da Jafar, kallonta yake tamkar ya ga sabuwar hallita. A hankali ta janye idonta ta fice daga cikin hall ɗin, da sauri Jafar ya miƙe ya kalli Safna ya furta. "One minute love." Bai jira amsarta ba ya bi bayan Uwani, a can wani ɗan dandamali ya hango ta. Zamanta babu jimawa ya hango wani matashin saurayi ya ƙarasa wurinta, sallama ya fara yi wa Uwani a hankali ta goge hawayenta ta amsa masa. "Mai kyau lafiya kike kuka kuwa?" Matashin ya furta a daidai lokacin da Jafar ya ƙarasa wurin. "Kaina ke ciwo!" Uwani ta furta a sanyaye. "Kai! Me kake yi a nan?" Jafar ya furta a tsawace. "Dama beb ɗin nan ce ta yi mini shi ne..." "Ku me ya sa wani lokacin ba ku da hankali ba kwa tantance matar aure da budurwa ne?" Da sauri matashin ya riƙe baki ya ce, "Mai gida don Allah ka yi haƙuri ban san tana da aure ba." Jafar bai amsa masa ba sai aika masa da harara yake yi. "Me ya fito da ke nan za ki zo kina kuka, har wani ƙato ya dinga ce miki mai kyau?" "Me ya sa ko korar mini saurayi?" Uwani ta wurga masa tambaya ita ma. Ran jafar ya sake ɓaci a ɗan tsawace ya ce, "Za ki amsa mini ko sai na ɓata miki rai." Uwani ta juyar da kanta gefe har lokacin hawaye take yi, Jafar ya sake zagayowa ta gabanta ya ce. "Ba tambayarki nake ba?" "Ni ma ai tambayarka na yi me ya sa ka korar mini saurayi?" Riƙe baki Jafar ya yi yana mamaki, yana shirin magana ya ji ta ci gaba da cewa. "Kai ma fa warewa ka yi a wuri daban kai da budurwarka kuna hira, ni ma ba sai ka bar ni na yi sabgar gabana ba." Ran Jafar a ɓace ya furta, "Da aurena a kanki ba ki isa ki yi mini wannan iskancin ba, sai ki bari ranar da na sauke igiyoyina uku daga kanki sai ki je can ki kula duk wanda za ki kula. Kuma ki tashi ki koma ciki ba na buƙatar ganinki a nan." Uwani yi ta yi kamar ba ta san me Jafar yake faɗa ba, ya sa hannu ta ƙarfi ya fiszo ta har ta kusa faɗawa kansa. A daidai lokacin Safna ta ƙarasa wurin don ta ji Jafar shiru bai koma ba, ganin abin da Jafar ya yi wa Uwani ya sa ƙirjinta ya buga da ƙarfi. A ɗan hargitse Safna ta haɗe fuska tana faɗin, "Baby me kake yi haka? Wace ce wannan?" Uwani ta wurga mata harara sannan ta ja tsaki, Jafar na shirin magana daga gefe suka ji Maimuna 'yar wurin Baba Mustafa ta ce. "Amaryarsa ce wataƙila sarautar ce ta motsa ya biyo ta yake lallaɓarta, kin san dramar Ya Jafar da Uwani ba ta ƙarewa. Ni ban san ma yadda zamansu yake ƙarewa ba, don wallahi na san watarana sai su cinna wa gidan wuta." Maimuna na gama maganar ta yi gaba tana murmushi, don ita sam ba ta san wace ce Safna ba. Uwani ta fisge hannunta daga jikin Jafar ta dubi Safna ta furta. "Sai ki yi nazari domin ganin buzu a masallaci ya ishi tinkiya ta yi hankali." Daga haka Uwani ta wuce ko waigensu ba ta sake yi ba. Safna ce ta ƙura wa Jafar ido da kallon tuhuma ta furta, "Wace ce wannan yarinyar? Kuma me ye alaƙarta da maganar da waccen ta faɗa?" Jafar ya ɗan saita nutsuwarsa ganin zancen da Maimuna ta faɗa bai shigi Safna ba, ya sakar mata murmushi ya ce. "Cousin ɗina ce, yarinyar ba ta da kunya and akwai wani yaro ɗan iska ne da iyayenmu suka hana ta kula shi. Ina fitowa nagan su a zaune suna hira, a kan na kore shi take neman ta yi mini rashin kunya. So kar ki damu da maganar Maimuna duk irin wasan abokan wasa ne ita ma cousin ɗina ce." Sai a lokacin Safna ta sauke ajiyar zuciya, ta ɗan saki murmushi ta furta. "Dama maganarta ba ta wani dame ni ba, because i trust you. Na san ko girlfriend ba ka da ita, to ma ta ya har za ka iya rayuwa da wata macen ba ni ba." Jafar ya yi saurin gyaɗa mata kai sannan suka koma ciki. Jafar tun da ya zauna hankalinsa na wurin Uwani don ya san yarinyar ba ta da hankali tsaf sai ta fita ta je ta kula samari a waje, har sai da Safna ta lura hankalinsa kamar yana wani irin. Uwani na shiga ta wuce wurin Mami ta ɗan sunkuya wurin kunnenta ta ce, "Mami wani ƙaton mutum mummuna a gate ya ce wai a kirawo ki zai yi miki fatan alheri." Rass! Gaban Mami ya buga, duk AC da ke wurin bai hana gumi ya keto mata ba. Ta yi ƙasa da murya ta ce, "Wane iri ne mutumin? Kuma kin tabbata abin da ya ce miki kenan?" Uwani ta gyaɗa kai ta ce, "Ni fa surarsa tsoro ta ba ni, yatsun hannuwansa bibbiyu ne fa. Ga shi saman tsakiyar kansa na ga har hayaƙi yake yi!" Da sauri Mami ta ce hayaƙi?" Uwani ta gimtse dariyar ta haɗe da gyaɗa mata kai. Ƙawayen Mami da ke wurin jin abin da Mami ta faɗa ya sa gabaɗaya suka ce, "Hayaƙi kuma? Me ye yake hayaƙi?" Uwani za ta yi magana da sauri Mami ta katse ta da cewar, "Wai bayan fitowarmu daga gida ne aka ga kitchen yana hayaƙi, amma Daddyn yara ya kashe dama gas ne ashe ba a kashe ba abinci ya fara ƙauri." Gabaɗaya suka furta, "Alhamdulillah, Allah Ya kiyaye gaba." Mami ta riƙe hannun Uwani suka tashi daga wurin sai da suka matsa daga wurin mutane sannan ta furta, "Maza koma ki zauna kuma kada ki faɗa wa kowa wannan maganar." Uwani ta bi Mami da kallo ganin yadda take kwantar mata da murya, Uwani ta koma mazauninta tana ci gaba da 'yan kalle-kallenta tana murmushi ƙasa-ƙasa. Auta ce ta ƙarasa wurinta ta ce, "Uwani ina kika je ne? Ki zo mu je mu yi rawa." Da kamar Uwani ta noƙe sai kuma ta bi Auta suka shiga cikin fili suka fara takawa a hankali, wani abokin Salim ne ya shiga ya fara yi wa Auta liƙi. Babu jimawa wani ma ya shiga ya fara yi wa Uwani liƙi, ganin irin kuɗin da suke zubarwa a kan Auta da Uwani ya sa Mc ya fara koɗa su yana faɗin. "A gaskiya wannan biki ya yi albarka, ga wasu abokan ango nan suma da alama sun yi kamun matan aure." Wani irin tuƙuƙin ɓacin rai ne ya mamaye Jafar, musamman da ya ji kalaman Mc. Ita kuwa Uwani ko a jikinta sai juyi take tana sakin murmushi. Sai da Uwani ta gaji don kanta sannan ta ja hannun Auta suka fita daga cikin filin, Muhsin ne ya biyo Uwani yana neman lambar wayarta. Nan take Auta ta shaida masa tana da aure, ba don ya so ba haka ya koma ya je ya zauna. Uwani na daga zaune ta bi ƙaton cake ɗin amarya da ango da kallo, ya ƙwayatu sosai kuma a tsaye ya kusa tsayinta don da gani an narka dukiya a jikinsa. Ta waiga ta hangi yadda Mami ke washe baki cikin farinciki. A fili Uwani ta furta, "Ya zama dole taron nan ya watse yanzun nan." Miƙewa ta yi ta kira Auta ta ce ta raka ta za ta yi fitsari, Humaira da Na'ima ƙawayen Auta suka ce za su raka ta don ita ma Na'ima fitsarin take ji. A ɗan zagayen hall ɗin banɗakunan suke guda uku a jere, sai dai wurin duhu gare shi ba kamar can wurin da mutane ke zirga-zirga ba. Daga ɗan baki-baki su Auta suka tsaya Uwani da Na'ima suka ƙarasa, Uwani dama babu wani fitsari da take ji kawai don ta tashi wurin da ƙura ne. Tana shiga banɗakin ta ƙwalla ƙara tana faɗin. "Wayyo kunnuwana! Auta suna fisgar ƙafata, wai kunnuwa za su cire. Sun ce duka sai sun fige kunnuwan mutanen wurin nan." Uwani ta fito daga banɗakin a guje tana doka ƙauren banɗakin da Na'ima take ciki. Tun Uwani ba ta gama ihu ba Auta da Humaira suka zuba a guje, Na'ima na jin haka ta fito a guje wando na saɓulewa don ko fitsarin ba ta gama ba ta ji ihun Uwani da abin da take faɗa. Sai da Uwani ta ga sun shige sannan ta yi tsalle ta sauke fiyus ɗin wutar wurin, ta kuma ƙarasa can bakin ƙofar hall ɗin da gudu a cikin duhu ta laluma ta tura ƙofar shiga hall ɗin ta datse ta. Lokaci ɗaya hall ɗin ya kacame da ihu masu kuka na yi masu kiran sunan Allah na yi. Mami kuwa dama tun lokacin da wutar wurin ta ɗauke take sakin fitsari ba ji ba gani, Uwani kuma ta fara bi tana gasa wa mutane mintsini wasu kuma sai dai ta sa takalminta ta wanka musu mari da shi. Sai dai ka ji ƙato ya zuba ihu yana cewa, "Wayyo sun mare ni." A haka ne Uwani ta ɗaga takalmi ta tafkawa Salim a fuska, cikin tashin hankali da galabaita ya furta, "Wayyo Allahna Shukra kin cuce ni, sai da na ce ba zan zo ba kika tilasta mini ga shi yanzu suna zo yage naman fuskata." Securities ɗin wurin ne suka buɗe ƙofar da ƙarfi ganin abin da yake faruwa ya sa suka fara haske-haske, ɗaya daga cikinsu ya zagaya ya ɗaga fiyus ɗin wutar lokaci ɗaya haske ya mamaye cikin hall ɗin. Kallon kallo kowa ya tsaya yana yi ganin yadda suka hargitse lokaci ɗaya, Jafar na ɗagowa ya gan shi saƙale a jikin Hajiyan Safna ga jakarta rataye a saman kafaɗarsa ta zagayo ta cikin kansa. Da sauri ya ja da baya a kunyace, ita ma Hajiyan Safna ta matsa gefe saboda kunya kamar ta nutse a ƙasa. Da Mami da Salim sai kallon juna suke ganin yadda suke dame fuskokinsu da zungureren cake ɗin amarya da ango, jin sanyi-sanyi a kan Mami ya sa ta kai hannu sai ji ta yi ta kwaso wani lafcecen cake a saman kanta. Tana waigawa ta hango gwaggwaron kanta ya yi cokoko a saman cake ɗin, Shukra kuma na maƙale da Mc sai da ta dawo hayyacinta ta diro daga bayansa, don shi ma bai san ya saɓa ta a baya ba saboda tashin hankali. Uwani na ankare da su ɗaya bayan ɗaya, ganin har lokacin a firgice suke ya sa ta manna a guje tana faɗi. "Ga su nan, ga su nan sun fara jan ƙafafuwan mutane, wayyo Allah ƙafata!" Ta yi hanyar gate a guje, ai kuwa a guje mutane suka rufa mata baya. Salim yana gudu babbar rigarsa na taɗe shi shi da abokansa, ita kuwa Shukra kafin ta je bakin ƙofa faɗuwar kusan biyar tana tashi. Mami ba ta jira ɗaukar ɗankwalinta a kan cake ba ta fita a guje zanin jikinta na ƙoƙarin kuncewa. Littafin kuɗi ne idan kina buƙata za ki biya 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wanaan layin 07062062624 idan littafi ya kammala cmplt doc 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Tamkar korarru ko waɗanda suka dawo daga wurin da wata tarzomar yaƙi ta tashi haka 'yan biki suka koma gida, wasu babu ɗankwali wasu babu takalma. Daddy na daga saman barandarsa yana karanta jarida ya fara jin bugun gate da ƙarfi kamar za a ɓalle ƙofar, yana kallo Lado ya buɗe musu ƙofa a yanayin yadda suka shiga ne ya sa ya fahimci wannan taron shi ma ba a wanye lafiya ba. Bayan da suka shiga suka ba wa Dada labari ban da dariya babu abin da take sheƙawa, Mami kuwa takaici da baƙincikin da ta shiga har ya fi na ranar kamu. Domin ba ƙaramin muzanta ta yi a cikin ƙawayenta ba, uwa-uba kuma yadda ƙananun maganganu suka dinga tashi. Jafar shi da Safna babu wanda ya nemi wani a lokacin da ƙurar ta lafa sai a washegari suka haɗu. Ita ma Uwani a wannan ranar a ɗakin Dada ta kwana don ta gaji tuɓus jikinta sai ciwo yake yi, zuciyarta fes take ji don ta san ko babu komai yadda Mami da Shukra suka tozartata suka wulaƙantata suka laƙa mata sata ita ma ta fanshe abin da suka yi mata. Don haka a ranta ta furta, 'Ai ko yanzu kasuwa ta tashi, Ɗankoli ya ci riba.' Tun da ta san babu wani taro da za a kuma yi sai kuma na ɗaurin aure. Washegari ne ya kasance ranar ɗaurin aure, kuma wurin ƙarfe goma sha biyun rana aka ɗaura auren Shukra da Salim. Ango ya zo da abokansa sai hotuna ake yi, Mami sai shiga ake ana fita cikin shigar alfarma. Wurin ƙarfe huɗu ne kuma Salim ya aiko da motoci aka ɗauki amarya da 'yan kai amarya, sai dai ko da wasa Uwani ba ta yi gigin bin 'yan kai amarya ba. Hajiyan Safna kuma da Safna suka fito da jakunkuna domin jirginsu ƙarfe shida na yamma zai tashi. Kafin su fito sai da Daddy ya yi mata godiya sosai, sannan ya nuna mata bayan kwana biyu zai nemi mahaifin Safna su yi maganar auren su Jafar, bayan ya warware tun mahaifin Safna yana fama da matsalar ciwon suga. Saboda a nazarin da ya yi duk abin da Mami ta yi babu laifin Jafar a ciki hasali ma ya yi masa biyayya ya auri zaɓinsu, kuma suna zaman lafiya don haka shi ma zai yarje masa ya auri zaɓin ransa. Sannu a hankali baƙi suka dinga watsewa kowa ya kama gabansa, Dada ma bayan bikin da kwana uku ta ce za ta tafi har da Uwani. Jin kalaman Dada ba ƙaramin farinciki ya dasa a zuciyar Jafar ba, da yake gabaɗaya suna zaune Dada take maganar Jafar da bai san da tonuwar asirin su Mami ba ya furta. "Ni fa tun da Allah Ya ga ina zaune da yarinyar nan da zuciya ɗaya kuma Dada duk wannan bai yi miki ba, kawai ki ɗauke ta ki tafi da ita. Ƙiri-ƙiri fa Daddy kana gani ta kwashe kuɗin wurinka..." Shewar da Dada ta saki ce ta katse Jafar, sai da ta bi Jafar da kallon harara sannan Dada ta zayyane masa duk abin da ya faru. Daddy na gama sauraron Dada ya ɗora da cewa. "Duk fa mahaifiyarka ta yi haka ne saboda waccen yarinyar Safna, dalilin da ya sa rannan na ce maka ba za ka aure ta. Amma na yi nazari na ga ba laifinka ba ne, sai dai a sannu zan ɗauki matakin da ya dace a kan ki Saratu." Mami ta yi tsilli-tsilli da ido ta gagara yin magana, takaici ya mamaye Jafar yana mamakin abin da Mami ta aikata. Bayan bikin Shukra da sati guda Jafar ya koma Lagos da aiki, a daidai kuma wannan lokacin ne aka nemawa Uwani makarantar da Auta take zuwa. An yi wa Uwani Interview wasu ta ci wasu kuma ta faɗi, hakan ya sa hukumar makaranta ta nemi da ta saka Uwani a JSS 2 Amma Daddy ya ce a saka ta a SS 1, Zai nema mata mai lesson a gida a dinga koya mata abin da ba ta gane ba. Da yake makarantar haɗe take Islamiya da boko ya sa Uwani ta samu sauƙin horon Mami, Asabar da Lahadi ne kawai babu makaranta. Ranar Asabar Teacher Nuhu ne yake koya mata ɓangaren boko, ranar Lahadi kuma Mu'allim Abubakar yake koya mata abin da ya shafi ɓangaren addini. Ana gobe Uwani za ta fara zuwa makaranta Daddy ya kira ta ɗakinsa, bayan ta zauna ya furta. "Mamana!" Uwani ta ɗago ta amsa sannan ya ci gaba da cewa. "Kin san dai ke yanzu ba yarinya ba ce ko Mamana? Kin ga yanzu za ki fara zuwa makaranta, kuma mun yi wa malamanku bayanin kina da aure. Ki tsaya ki yi karatu sosai, kin taɓa ce mini aikin tuƙin jirgin sama kike so ko?" Uwani ta ɗan yi farr da ido sannan ta yamutsa fuska ta ce, "Gaskiya Daddy na canza, ni fa ina jin 'yar sanda zan zama don gaskiya na gaji da barazanar da Ya Jafar yake yi mini da bindigi. Ka ga idan na zama 'yar sanda sai mu nuna juna da bakin bindiga idan ya so ko harbe juna sai mu yi, ba shi kenan ba kowa ya huta?" Daddy ya yi murmushi ya ce, "Mamana kenan, aikin ɗan sanda ai ba don a yi wa juna barazana ake yi ba. Domin kare dukiya da rayukan al'umma ne. Ki dai yi nazari Mamana ki zaɓi wani aikin da kike ganin ya fi." Uwani ta gyaɗa kai sannan Daddy ya ce. "Alƙawarin awakinki da na yi miki kuma yau zan sa a fara aikin runfar da za a yi musu, zuwa nan da kwana huɗu na tabbata an gama komai sai na sa a kwaso miki su. Amma fa ba za a kawo kejin nan naki ba, zan sa dai a haɗa miki wani na ga wancen ya tsufa ya ma sunan zakaran nan na ki?" Da sauri Uwani ta ce. "Wai Lawan mijin fanteka? Allah sarki Lawan wallahi Daddy na yi kewarsu, na san suna can suna saka Dada Magana." Daddy ya yi murmushi sannan suka ci gaba da hira. A cikin kwanaki ƙalilan aka yi wa Uwani wurin mazaunin awakinta, kuma a cikin waɗannan kwanakin ne Daddy ya sa aka ƙara gyara masa ɗayan ɓangaren da ke kallon na Mami. Mami ta yi mamaki har ta gagara shiru a ranar da ta ga Daddy ya sa an kwaso mata wasu tarkacen da ta zuba a wurin. "Daddyn yara ni fa ban gane wannan gyaran da kake yi ba, yaushe muka dawo gidan nan da za a ƙara gyara wannan sashen?" Daddy ya ɗan yi murmushi ya furta. "Saratu don zan gyara muhallina sai kin tutsiye ni da tambayoyi? Dama yau nake shirin sanar da ke Juma'a me zuwa ne za a ɗaura mini aure, ya kamata a sama miki ƙanwa tun da sannu a hankali yaran nan tafiya suke yi..." "Ƙundun uban can! Mamman ni za ka tozarta ka wulaƙanta. Da tun da ƙuruciya ba ka yi mini kishiya ba sai yanzu da girma ya zo? Wallahi ba ka isa ba sai dai ka zaɓa ko ni ko matsiyaciyar da za ka auro." Daddy ya saki murmushi sannan ya nuna mata hanya ya furta, "Saratu ai ƙofa a buɗe take ni ba zan yi miki dolen zama da ni ba. Kuma idan muna da yawanci kwana aurena babu fashi, gara ma ki kwantar da hankalinki don ni ba zan yi auren nan don na wulaƙanta ki ba..." Kukan da Mami ta saki ne ya katse kalaman Daddy, ta miƙe rai a ɓace cikin kuka ta ce. "Wallahi namiji ɗan kunama ne tsakanina da kai ban yafe ba." Mami ta fice tana doko masa ƙofar da ƙarfi. Murmushi Daddy ya yi a fili ya ce, "Saratu ko rigima." Abuwa 'ya ce a wurin marigayya Fatsime ƙanwar Dada, kuma tun gabannin auren Uwani ta dawo wurin Dada da zama sakamakon ta gama takabar mijinta da ya rasu. Shekararta Talatin da biyar, kuma duk tsawon shekarun da ta shafe da mijinta Allah bai taɓa ba ta haihuwa ba. Tun bayan bikin su Jafar Daddy ya fara gabatar da kansa a wurin Abuwa sai dai nauyinsa ya sa ta gagara amincewa, sai daga baya ne sannan ta ce masa su yi Addu'ar Allah Ya zaɓa abin da ya fi zama alheri. Kuma ko Dada ba ta san abin da yake tsakaninsu ba sai daga baya, a wannan lokacin ne ragowar mutanen cikin gidan suka fara jin raɗe-raɗin abin da yake faruwa. Da yake Mami ba wani fuska take ba wa facalolinta ba shi ya sa ko a tsegumi babu wanda ya taɓa tunkararta da maganar, saboda sanin wulaƙancinta ya sa kowa yake kama mutumcinsa. Abuwa ta kasance mace mai sanyin hali ba ta hatsaniya ko kaɗan, tana da haƙuri sosai sai dai ba ta ɗaukan raini ko cin zarafi. Ƙaunar da Dada take yi wa 'yar uwarta Fatsime ya sa bayan mutuwarta ta dawo da ita kan Abuwa, saboda duk cikin 'yan uwanta ta fi shaƙuwa da Fatsime tun da a hannunta ta taso. Tun ranar da Daddy ya yi wa Mami maganar auren ta ɗauki fushi da shi, ko gaisuwa ba ta shiga tsakaninsu. Don ma Jidda da Auta na kwantar mata da hankali, lokacin da Mami ta kira Shukra ta faɗa mata haka ta yi ta zuga ta tamkar ita ce uwarta. Shi kuwa Jafar da ta sanar da shi addu'a kawai ya ce ta yi a kan Allah Ya sa ta gari za a kawo mata. Don shi a ganinsa bai ga abin tashin hankali ba, jin Jafar bai ba ta wani goyon baya ba ya sa Mami ta katse wayarta ko da ya kira ta ba ta ɗauka ba. A ranar Juma'ar ne aka ɗaura auren Daddy da Abuwa, sai kuma na na Madina da Goggon su Sabi'u. Da yake ba wani taro aka yi ba ya sa ko Uwani ba ta je gidan ba, don Daddy cewa ya yi ba za ta dinga katse makaranta tana wayo ba. A farkon tafiyar Jafar Auta ke zuwa tana taya Uwani kwana, Daddy da kansa ne ya ce ta dinga taya ta kwana, amma tun ranar da ya faɗa wa Mami zai yi aure ta dakatar da ita. Da yake Mami ba ta bada fuska a game da auren Daddy ba ya sa ko wacce ya aura ɗin ma ba ta sani ba, sai a washegarin ranar da Abuwa ta tare. Saboda ko da aka kawo Abuwa Daddy ya yi juyin duniya Mami ta fito ya yi musu nasiha ta ƙi. Mami na fitowa falo a lokacin ita ma Abuwa ta fito cikin doguwar rigar atamfa sai zuba ƙamshi take, ganin Mami ya sa ta saki fuska tana faɗin. "Aunty Saratu ina kwana!" Sai da Mami ta ƙare mata kallo tun daga sama har ƙasa sannan ta taɓe ta ce, "Riƙe gaisuwarki Abuwa kike ko wa? Dangin mijin sarakan munafurci wato har an samu wurin zama a wurin kishiyata, za ki ɗebo guntum munafurcinki ki ce wani ina kwana? Da ban tashi lafiya ba za ki gan ni haka? Sannu a hankali da ita amaryar da ku zan haɗa su in ci abu ta kazar ubanku." Abuwa na tsaye tana jin duk abin da Mami take faɗa, Daddy ya ƙarasa wurin ya furta. "Kafin dai ki haɗa dangin nawa da matar da na aura ya kamata ki san matsayi wacce ke gabanki, Saratu me ya sa kike haka ne?" Mami ta yi ƙuri tana kallonsa, Daddy ya nuna musu doguwar kujera yana faɗin. "Saratu zo ki zauna, ke ma Zainab ki zauna." Sheƙeƙe Mami ta kalle shi ta watsar ta yi gaba har ta kusa fita a tsawace Daddy ya ce. "Wallahi Saratu idan kika saka ƙafa kika fita sai ranki ya yi mummunan ɓaci." Ganin yanayin ɓacin ran da ke kwance a saman fuskar Daddy ya sa Mami ta koma ta zauna, jiki a sanyaye Abuwa ita ma ta zauna. "Dalilin da ya sa na tara ku a nan don na tunasar da ku matsayin kowacce a cikinku..." Da sauri Mami ta katse shi. "Ban gane me kake nufi ba Daddyn yara." Daddy bai kula ta ba ya ci gaba. "Zan fara da ke Saratu ke ce babba, ke ce uwar 'ya'yana kuma ban yi auren nan domin na wulaƙanta ki ko don kin gaza ba. Kuma ba don ba na sonki ko ba na ƙaunarki ba, sai don ra'ayin kaina. Ki riƙe girmanki a matsayinki na babba, ba na son jin wani tashin hankali daga gare ki." Daddy ya waiga wurin Abuwa ya ce. "Ke kuma Zainab ke ce ƙarama, ban auro ki domin ba na ƙaunar matata ba ko don ta gaza mini ba..." A zabure Mami ta miƙe tsaye tana nuna Abuwa ta furta. "Wannan ita ce kishiyar tawa? Wato kace auren cin amana aka yi, ai shi kenan dama ni na jima da sanin Dada ba ƙaunata take yi ba. Shi kenan burinta ya cika tun da ta haɗa ka da 'yarta, don haka ka riƙe kalamanka babu wani amfani da za su yi mini." Mami na gama faɗar haka fuuuu ta shige ɗakinta, Abuwa ta sunkuyar da kai ƙasa idanunta suka ciko da ƙwallah ta furta. "Daddyn Jafar abin da na jima ina tsoro kenan shi ya sa tun farko na ƙi amincewa da maganar auren nan, ba na son na zama silar tarwatsewar gidanka. Don Allah..." Daddy ya yi saurin katse ta, "Ba na son ƙara jin wata makamanciyar magana irin wannan, tashi ki shiga ɗaki zan sa a kawo breakfast." Babu musu Abuwa ta shiga ɗakinta, Daddy ya miƙe ya nufi ɗakin Mami. Kamar ƙaramar yarinya haka ya same ta a kan gado tana gursheƙen kuka, zama ya yi a gefenta ya janyo ta da ƙarfi ta fara kiciniyar fisgewa. Riƙe ta ya yi sosai suna fuskantar juna, Daddy ya ciro wani handkee ya ba ta sannan ya furta. "Goge fuskarki!" Shiru Mami ta yi ganin ba ta da niyyar goge fuskarsa ya sa ya ɗauka ya goge mata sannan ya furta. "Me ya sa kike son saka wa kanki damuwa a kan abin da bai taka kara ya karya ba? Saratu!" Daddy ya kira ta da wata irin murya. "Ke ce matata ta farko wacce muka yi aure tun ƙuruciya, ke ce kuma uwar 'ya'yana wacce duniya ta san ni da ita. Na san wace ce ke kin san waye ni, ba na jin ko mahaifiyata ta san waɗansu ɗabi'un nawa kamar yadda kika san ni. Ta yaya kike tunanin zan auri wata mace domin na tozarta ki ko na wulaƙanta ki? Saratu da zan wulaƙanta ki yau shekara sama da talatin da aurenmu, ban wulaƙanta ki ba sai yanzu? Ina ƙaunarki kin sani..." "Amma me ya sa Daddyn yara?" Mami ta katse shi. "Me ya sa tun tuni ba ka yi auren ba sai yanzu? Me ya sa ba ka fita duniya ka auri bare ba sai a danginka? Allah Ya sani ba zan iya jure ganin ka tare da wata ba, idan na furta hakan na yaudari kaina. Don Allah ka rubuta mini takardata na haƙura da kai Daddyn yara." Murmushi Daddy ya saki ya furta. "Saratu kenan! Ke a gajeren hankalinki kina ganin zan iya sakinki a yanzu? Ki yi nazari da kyau don kin fi kowa sanin wane ne ni idan har zan rabu da ke da tuni na jima da sakinki. Ki yi tunani da kyau kin san dai zan yi adalci a tsakaninku." Daddy na kai wa nan ya fice daga ɗakin. Haka zaman Mami da Abuwa ya ci gaba da tafiya, Mami ba ta kula ta koda ita ta yi mata magana. Hatta shi kansa Daddy ta zame al'amuranta daga gare shi, daga gaisuwa babu abin da yake haɗa su koda ranar girkinta ne, Auta tana ba wa Abuwa girma daidai gwargwado Jidda ce dai take ta ya Mami kishi sai kuma Shukra idan ta zo gidan, amma hatta Ibrahim idan suka haɗu yana ba ta girmanta. Zaman Abuwa a gidan sai ya kawo wa Uwani samun rangwame da sauƙi sosai, sai ɗan abin da ba a rasa ba domin da gayya Mami take saka Uwani wani aikin don tana taƙamar ita mahaifiyar Jafar ce. Kuma ta ci alwashin yadda Dada ya dasa mata baƙin cikin zama da kishiya, ko da malamai sai ta sa Jafar ya ƙara aure ko da kuwa Safna ba ce. Ballanta ta tabbata Safna ita ce birnin zuciyar Jafar. Tun da Jafar ya sa ƙafa ya tafi Lagos sai da ya shafe sama da wata takwas ba tare da ya zo Kano ba, kullin Daddy ya yi masa maganar zuwa gida sai ya ce masa aiki ne ya yi masa yawa, ko ya ce an tura shi wani garin aiki. Har sai da ran Daddy ya ɓaci ya ce masa tun da ba zai dawo ba zai nemawar Uwani transfer makaranta ta bi shi Lagos ta ci gaba da karatunta a can. Abin da Daddy bai sani ba kuma, Mami ce ta hana Jafar zuwa har sai da ya sanar mata da saƙon Daddy sannan ta amince masa, don ta san idan ta bari Uwani ta bi shi Lagos komai zai iya faruwa, kuma ta samu 'yancin cin gashin kanta a ɓangare ɗaya kuma ta wargaza maganar auren Jafar da Safna. Tun da ta san ko hauka ne a kan Hajiyan Safna ba za ta bari Safna ta auri Jafar ba, matuƙar ta san yana da aure. A ranar wata laraba ne Jafar ya ce zai zo, amma da yake kwana suke yi a hanya sai alhamis zai iso Kano. Daddy ne ya sanar da Aunty wato Abuwa da su Uwani suke saka mata. A ranar alhamis kuwa cewa ta yi Uwani ba za ta makaranta ba saboda ta yi ɗan gyare-gyaren da ba a rasa ba tun da mijinta zai dawo. Daddy bai yi faɗa ba, sai ma daɗi da ya ji ganin yadda Abuwa ke haɗa Uwani da Auta take yi musu abu tare kamar 'ya'yan cikinta. Abuwa da kanta ta kai Uwani wurin wankin kai da yake me kufan gashi ce tuni kanta ya haɗe, daga nan ta kai ta gidan lalle ita ma aka zane mata ƙafa da hannunta. Uwani ta fito shar ta yi kyau, bayan sun dawo gida ta sa Uwani ta sake gyara gidanta aka saka turaren wuta, ta ko ina ƙamshi sai tashi yake. Kimanin ƙarfe bakwai na dare Jafar ya ƙaraso gida, sashen Mami ya fara shiga ya gaishe ta sannan ya fito falo suka haɗu da Aunty suka gaisa. Jafar har zai sauka Mami ta furta. "Ga ruwan wanka nan a public toilet na sa an kai maka, ya kamata ka yi wanka ka ci abinci." Sai da Jafar ya ɗan sosa kai sannan ya amsa, ran Aunty ba ƙaramin ɓaci ya yi ba. Don haka ta shige ɗaki ta bar su a nan tun da ta san da biyu Mami ta yi haka. Jafar yana cin abinci yana son ya tambayi Uwani yana tsoron faɗan Mami, tun a Lagos yake jin kewarta musamman idan ya tuna tsiwa da rashin kunyarta. Ita kanta Mami ta lura da hankalinsa ba ya wurinta. Suna nan zaune Daddy ya shigo ganin Jafar zaune yana cin abinci ya sa ya ɓata fuska ya furta. "Kai Jafar ina matarka ka zauna cin abinci a nan?" Shiru ya yi Mami za ta yi magana ya dakatar da ita. "Tashi ka tafi ɓangarenka." Jafar kamar jira yake yi ya miƙe ko jakarsa bai ɗauka ba ya nufi sashensu. Uwani tun da ta ji shigowar Jafar gabanta ya fara faɗuwa ba ta san dalili ba, ta sake kallonta a gaban mudubi tana ɗan jujjuyawa haɗe da riƙe ƙugu. Gown ɗin atamfa ce a jikinta ba ƙaramin kyau ta yi mata ba, tana ɗagowa ta hangi Jafar a tsaye yana bin ta da kallo ta cikin mudubi ba tare da ta ji shogowarsa ba. Wata irin kunya ce ta kama ta wacce ita kanta ba ta san ta mece ce ba. Tana nan tsaye ta ji ya riƙo hannunta a hankali ta ɗago da kanta, karaf suka haɗa ido. Jafar ya sakar mata wani lallausan murmushi cikin sanyin murya Uwani ta furta. "Ya Jafar ashe ka shigo?" Littafin kuɗi ne akan 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar biya ta wannan layin 07062062624 Idan littafi ya kammala cmplt 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Ya yi mamakin yadda ta tsara kwalliya ta hankali ba irin wacce ya tafi ya bar ta tana yi ba, watanni takwas da bai ganta ba ya ga har girma da kyau ta ƙara yi. Jin bai amsa mata ba ya sa ta sake ɗago dararan idanunta ta dube ta furta. "Sannu da zuwa!" Mamaki ne ya sake kama shi wai har Uwani ta san ta ce masa wani sannu da zuwa? Ya ɗago haɓarta suna kallon juna ya furta, "Faɗa mini me ya sa kika takurawa Daddy ya ce sai na dawo?" Ɗan zaro ido waje ta yi ta ce. "Ni kuma? Allah ban taɓa ce masa ya yi maka magana ba, ni fa wallahi idan ba ji na yi kuna waya da Mami ba mantawa nake da kai." Uwani ta yi maganar zuciyarta ɗaya, ƙirjinsa ya ji ya buga bai san dalili ba. Haka kawai ya ji bai ji daɗin kalamanta ba. "Me zai dame ka tun da dama ba auren soyayya kuka yi ba? Ko ka manta da Safna ita ce zaɓin ranka?" Zuciyarsa ta gargaɗe shi. Ajiyar zuciya ya sauke a fili ya ce. "Shi kenan ai sai na koma, ni da farko ma da na ganki na ɗauka kin yi hankali ashe dai har yanzu da sauranki." Jafar ya yi maganar yana fita Falo. "Kullin dai abin da Aunty take faɗa mini kenan, to ni me nake yi saboda Allah? Haka fa ta takura har lallai na yi yau, to kai ko me zai birge ka a wani lalle?" Ba ki sake yake bin Uwani da kallo, a farkon shigarsa ɗakin sai ya rantse Uwanin da ya gani da bambamci da waccen da ya bari a baya. Sai yanzu ya sake tabbatar da mai hali dai ba ya sauya halinsa. "To wai Ya Jafar ina tsarabar Lagas ɗin? Ko haka ka taho fankan-fayau?" Shiru ya yi yana ƙare mata kallo, jelar gashinta ya hango ta baya da sauri ya miƙe tsaye yana ɓata fuska ya ce. "A gidan Uban wa kika koyo saka ƙarin gashi?" Jafar ya yi maganar yana fisgar gashin Uwani da ƙarfi, cikin jin zafi ta ƙwalla ƙara sai ga ɗan kwalinta a ƙasa. "Ni fa wallahi shi ya sa tun da Aunty ta ce za ka dawo raina yake ɓaci, na san zalintata za ka yi ta yi idan ka dawo. Wallahi ba don Malam Gali ya ce zagin mijin haramun ba ne da sai na ce Allah ya isa." Jafar bai bi ta kan kalaman Uwani ba ya sa hannu yana shafar gashinta wani sabon yanayin na zaga ilahirin jikinsa, da ido take bin sa da kallo a shagwaɓe ta ce. "Ni dai don Allah ka bar wargaza mini gashi kusan dubu hudu Aunty ta ba wa 'yar bayerabiya ta gyara mini shi." "Yaushe gashin ki ya fito?" Jafar ya furta cikin suɓutar baki. Uwani ta taɓe baki ta ce, "Shi gashi yana da ranar fitowa ne? Ni ma ganinsa kawai na yi a haka?" Jafar ya tsuke fuska zuciyarsa na gargaɗinsa a kan zaƙewar da gangar jiki da ruhinsa ke yi a kanta. Kamar yadda Aunty ta tsara mata haka Uwani ta yi, abinci ta kawo ta zuba masa yana cikin ci ta miƙe za ta fita. Jafar ya wurga mata tambaya. "Ina za ki?" Uwani ta washe baki. "Duk fa bayan sallar Isha'i a wurin Aunty muke zama tana gyara mana hadda." Kamar ya yi mata magana sai kuma ya rabu da ita, Uwani ta fice hankalinta kwance ta yi ɓangaren Aunty. Aunty na zaune a falonta sai ga Uwani da ke ta zuba ƙamshi. "Me ya kawo ki nan kuma Uwani?" Uwani ta washe baki, "Haba Aunty zuwa na yi biya hadda, ina Auta ne ba ta zo ba?" "Ungo nan Uwani." Aunty ta yi mata daƙuwa da hannu sannan ta ci gaba. "Mijinki ya dawo ɗazun nan ki zo nan wani biya hadda wurina." "Aunty shafa mini kai yake yi yana wargaza mini gashi duk tsadar kuɗin da aka biya fa." Salati Aunty ta ɗauka ta ce. "Uwani ni kam yaushe ne za ki yi hankali wai, dan gidanku saboda wa na kai ki gyaran gashin? To kin ga ni yanzu mijina zai shigo, tun wuri ki wuce wurin mijin naki sai ki ce ya biya miki irin tashi haddar." Cikin fushi Uwani ta fice ko sallama ba ta yi wa Aunty ba. Tana shiga ta samu Jafar har ya gama cin abinci, ganin yanayin da ta shiga da shi ya sa ya tambaye ta. Ta ba shi amsa a taƙaice, "Aunty ce ta koro ni wai na zo ka biya mini haddar! Ni kam Ya Jafar wai izunka nawa ma? Ƙila ma fa na wuce ka ko?" Jafar ya yi fakare yana kallon Uwani, sai da ta zauna sannan ya ce. "Uwani wai yaushe na zama sa'anki ko abokin wasanki? Jahili kika ɗauke ni ko me?" Murmushin mugunta ya saki sannan ya furta. "Idan Allah Ya kai mu gobe za mu fara biya hadda amma ki sani duk gyara ɗaya na yi miki ranƙwashi biyu!" Shiru Uwani ta yi tana nazari don ta san tana da 'yan kurakuren a wasu wuraren, amma gudun kada Jafar ya rainata ya sa ta ce. "Allah Ya kaimu amma fa ka sani wallahi idan ba ka ci ni gyara ba sai na yi maka rankwashi goma!" Da sauri Jafar ya amsa mata. A wannan daren dai zaman Uwani da Jafar babu yabo babu fallasa, sai wauta da Uwani ke yi masa wani ya yi tsaki wani kuma ya yi murmushi. Bai san me ya sa ba a yanzu dai ya daina jin ƙyamarta da haushinta. Amma sai ya alaƙanta haka da sauyin da ya gani a tattare da ita, idan kuwa Aunty Zainab ce ta mayar da ita haka ba ƙaramin jahadi ta yi ba duk da a wasu al'amuran da Uwani akwai ragowar gyara. Washegari tun da sassafe Uwani ta tashi ta gyara gidan ta ɗora musu breakfast kamar yadda Aunty ta faɗa mata, bayan ta gama komai ta faɗa ta yi wanka. Wasu ƙanan kaya riga da wando ta saka marasa nauyi, don tun da ta tashi take jin ciki da mararta na ciwo ƙarfin hali kawai take yi. Jafar bai farka ba sai wurin ƙarfe goma na safe saboda gajiya, ya yi mamakin yadda ya ga ko ina fes ga ƙamshi yana tashi. Toilet ya faɗa ya shiga wanka bayan ya shirya Uwani ta nuna masa breakfast, har lokacin bai daina mamakinta ba. Zama ya yi ya fara ci kamar dai ya ce ta zo su ci tare don va ƙaramin kyau ta yi masa ba sai kuma ya basar, don ba ya son abin da raini zai ci gaba da shiga tsakaninsu. Uwani na nan zaune ta ji mararta ta sake karta mata da sauri ta miƙe ta nufi banɗaki, ta ɗan jima a ɓanɗakin ta fito fuska shaɓe-shaɓe da hawayen. Kan kujera ta koma ta zauna ba a yi minti biyar ba ta sake komawa banɗaki, haka Uwani ta dinga zarya tun Jafar bai ankara da ita ba har ya ɗago ya dube ta lokacin da za ta koma banɗaki. "Lafiya wai kike zaryar toilet?" Baki sake yake bin Uwani ganin yadda fuskarta ta kumbure lokaci ɗaya. "Me yake damunki?" Ya sake wurga mata tambaya. Uwani ta sake ɓarkewa da kuka ta faɗa banɗaki, a wannan karon da ta fito can kusurwar bango ta maƙure ta saki wani marayan kuka. Tsaki Jafar ya yi a ɗan tsawace ya ce, "Wai me yake dumunki ne?" Uwani ta share ƙwallar idonta ta ce. "Don Allah kira mini Dada mu yi bankwana da ita." "Bankwana wane iri?" Uwani ta cusa kanta a cikin cinyoyinta ta sake rushewa da kuka, Jafar tashi ya yi ya leƙe banɗakin ya gama haske-haske da dube-dubensa bai ga komai ba. Yana nan zaune Uwani ta miƙe ta furta. "Tun da ba za ka kira mini ita ba bari na je Aunty Zainab ta kira mini ita, tun da dai dama kai ne za ka yi sanadiyyar mutuwata." Kan Jafar ya sake ɗaurewa Uwani za ta fita ya yi saurin dawo da ita, wayarsa ya ɗauko ya latsa lambar Dada ko uffan bai ce ba ya miƙa wa Uwani. Daga can ɓangaren Dada ta furta. "Waye haka ya kira ni da farar safiya? Ni dai na san Mamman ba ya yi mini wannan kiran ballantana ya tashe ni daga bacci, wai Jafaru bashi na ci ban biya ka..." Jin kukan Uwani ya katse maganar Dada, da sauri ta ce. "Wa nake ji yana kuka kamar Uwani, ina ce dai Mamman da iyalansa duk lafiya ƙalau suke ko?" Uwani ta tsagaita da kukan ta ce. "Ni dai ki yafe ni Dada, wallahi mantawa na yi shaf da gargaɗinki har na ba wa Ya Jafar fuska yanzu ga shi alamun mutuwa sun bayyanar mini yau da safe." Uwani na gama magana ta rushe da kuka. Dada ta yi jim sannan ta ce, "Ke Uwani ita mutuwar ce ta nuna miki alamu kamar ta haɗa iri da Umaru?" Uwani ta ja majina ta ce, "Wallahi da gaske nake miki mutuwa zan yi Dada, tun ɗazu alamomin mutuwar suke ƙara bayyanar mini." Dada da sauri ta ce. "Maza miƙa wa Jafaru wayar." Ba musu ta miƙa masa wayar Dada ta tambaye shi, shi kansa iya abin da ya sani ya sanar da ita, Dada ta ce maza ya kaita wurin Abuwa ƙila ta faɗa mata abin ke damunta. Sai da Dada ta katse Uwani ta tashi ta sake faɗa wa banɗaki, bayan ta fito ta je kan kujera ta sake rushewa da kuka. Jafar Ya yi mata magana suka nufi sashen Aunty a lokacin Mami na ɗakinta, a falo Jafar ya zauna jikinsa a sanyaye don kalaman Uwani ba ƙaramin faɗar masa da gaba suka yi ba. Sai da suka gaisa ta ga Uwani fuska a kumbure, Jafar ya zayyane mata komai. Aunty ta sake tambayar Uwani, sai da Uwani ta sake goge ƙwallah a lokacin fitowar Daddy kenan ta fara magana. "Wallahi tun da na zo duniya ban taɓa tunanin Ya Jafar riƙaƙƙen ɗan iska ba ne sai yau!" Rass! Ƙirjin Jafar ya buga, a hankali Jafar ya saci kallon Daddy. Ita kuwa Uwani ta ci gaba. "Dama da daɗewa Dada ta ce mini ba a ba wa maza fuska wallahi tsautsayi ya sa nake kula Ya Jafar, to ni dai ga abin da Dada ta faɗa ya zo kaina dama ta ce duk mace mai kula maza 'yar iska take zama, kuma alamun mutuwa na bayyana a jikinta shi kenan a ranar za ta mutu." Kuka ya ci ƙarfin Uwani, Daddy na shirin yin magana Uwani ta share hawaye ta ci gaba da cewa. "Tun da garin Allah ya waye nake fitsarin jini, kuma dama Dada ta ce wannan ne alamun mutuwa na farko jinina yana ƙarewa shi kenan sai dai a ɗauki mushena a kai daji a wurgar kura ta cinye." Uwani na zuwa nan a maganarta ta sake fashewa da kuka, cikin kuka ta furta. "Ni dai Ya Jafar ya cuce ni ya cuci rayuwata shi kenan Dada ba za ta ga 'ya'yana ba, wayyo Allah mutuwa za ta ɗauke Uwani." Tun da Uwani ta fara magana da Daddy ya fahimci inda zancen ta ya dosa yake murmushi don ba ƙaramin dariya ta ba shi ba, kuma wannan ya sake tabbatar masa da irin zaman da suke yi ita da Jafar. Kallon Aunty zainab ya yi da ke riƙe da baki ya furta. "Auntyn yara ga 'yarki nan ki ji da ita, kai Jafar ta so mu je." Tamkar kazar da aka tsamo daga ruwa haka Jafar ya miƙe yana sunne kai ƙasa, don da ya san abin kunyar da Uwani za ta yi kenan da ko harabar gidan ba zai biyo ta ba. Suna fita Aunty Zainab ta ja Uwani ɗaki ta furta, "Uwani wallahi yau na sake tabbatar da har yau da sauranki, gaskiya riƙon kaka daban yake. Amma hakan ma da Dada ta yi miki duk cikin tarbiyya ne." Nan da nan Aunty Zainab ta yi wa Uwani duk bayanin da ya dace, da yadda za ta gyara jikinta. Sai bayan da Uwani ta gama sauraronta ta ce. "Wai Aunty dama wannan shi ne duk bayanin da Malam Gali yake yi mana a Ahalari?" Aunty Zainab ta gyaɗa mata kai. Ko da Uwani ta koma sashenta ganin babu fuska a wurin Jafar ya sa ta taɓe baki ita ma ta fara ɗaure fuska, don gudun kada ya rainata. A haka dai rayuwarasu ta ci gaba babu yabo babu fallasa, kwanan Jafar bakwai a Kano su Daddy suka je gidan yayan mahaifin Safna da ke Unguwar sallari suka kai kuɗin auren Jafar da ita. Farinciki wurin Mami ya ƙi musaltuwa don hatta Daddy ya lura da yanayin da take ciki, a ɓangare Jafar da Safna kuwa bakinsu ne ya ƙi rufuwa. Uwani ta yi mamakin sauyin da ta gani a wurin Jafar, duk da bai ce mata uffan ba amma ta fahimci yana cikin farinciki. A ranar da magriba Uwani ta je wurin Aunty Zainab don shi ma Jafar yana wurin Mami, Aunty ta lura da yanayin Uwani da alama ba ta san abin da yake faruwa ba don haka ta same ta tana faɗin. "Uwani ina son ki buɗe kunnenki da kyau ki saurare ni, kuma duk abin da za ki ji ba na son sakarci ko shashanci." Uwani ta gyaɗa kai gabanta na faɗuwa. "Ɗazu Daddynku yake ce mini shi da su Yaya Inusa sun kai kuɗin auren Jafar da Safna." Dam! Ƙirjin Uwani ya buga, Aunty Zainab ta lura da yanayin da ta shiga ta ci gaba da cewa. "Don haka ina son kin kwantar da hankalinki hakan ba yana nufin mijinki ba ya ƙaunarki ba, shi ya sa a kullin nake son ki ajiye wannan sakarcin na ki a gefe ki kama mijinki ta yadda ko wata ta zo ba za ta nuna miki komai ba, Jafar namiji ne kuma mijin mace huɗu ko bayan ya auri Safna yana da damar auro wasu matan biyu. Ba a tsayar da lokacin auren ba tun da na ji Daddynku ya ce za ta je ƙaro karatu India, za ta yi shekara ɗaya da rabi zuwa biyu sai ta dawo za a yi bikin." Hawaye bibbiyu ne suke bin fuskar Uwani saboda wani irin ɗaci da take ji a ranta, amma da za a tambaye ta ita kanta ba ta san dalili ba. "Ni fa ban zaunar da ke domin ki yi mini kuka ba, ke ma fa mace ce Uwani. Shawara ɗaya zan ba ki da ki jajirce wurin neman ilimi tun da kin ga abokiyar zamanki ba ta zauna ba, ko kina son ki zama koma baya ne?" Uwani ta girgiza kai tana share hawaye, ta dubi Aunty Zainab ta ce. "Amma Aunty bai gaya mini ba fa! Abin da ya ba ni haushi kenan." Uwani ta faɗa tana ƙoƙarin kare kanta, don ba ta son a fahimci saboda zai yi auren ne take kuka. Aunty Zainab ta jima ta yi wa Uwani nasiha sosai sannan ta ɗan fara jinta da hira, saboda ta kawar mata da damuwar da ta ga tana ciki. Uwani ko da ta koma ɓangarenta ba ta nuna wa Jafar ta san da maganar ba, shi ma kuma bai sanar da ita ba. A haka har ya ƙare kwanakin hutunsa, da zai koma ne Daddy ya sa shi ya saya wa Uwani waya don su dinga magana da ita. Sannu a hankali rayuwa ta ci gaba da tafiya, Uwani ta watsar da koma ta kama karatunta sai kuma kiwon awakinta da take yi. Abin da ya fara damunta bai wuce sabon al'amarin da ya fara ɓullowa a cikin kejin awakinta ba, ranar wata talata ta dawo daga makaranta kafin ta shiga sashenta ta leƙa kejin su Lawan da kuma awakinta. A wajen kejin ta hangi wata baƙar kazarta da take yin ƙwai a sheme a ƙasa an yanka ta, tana shirin shiga sashen su Mami Lado ya ƙarasa ya furta. "Barka da shigowa Uwani, dama na ji shigowarki ina banɗaki. Ɗazu Hajiya ta kira ni ta ce a yanka kazar nan saboda wannan 'yar baƙar za ta kasa, ga ta nan da alama tana da albarka amma lokaci ya yi." Saboda takaici Uwani ba ta tanka masa ba ta yi sashen Mami, tana tambayarta. Abin da Lado ya faɗa mata shi ta maimaita mata, haka ne ya dinga faruwa sai Uwani ba ta nan ko tana cikin sashenta sai a kira ta a ce ga kaza ko zakara can an danne za a yanka saboda sun kasa. Da Uwani ta nuna ba ta son a dinga yanka mata, sai kuma ta koma ganin gawar kaza ko zakara a cikin kejin, a wannan lokacin hankalinta ba ƙaramin tashi ya yi ba saboda kajinta da suka ɗauko hanyar ƙarewa. Aunty ce ta ci gaba da tausarta tana ce wa ta ci gaba da addu'a tana faɗa wa Allah kukanta, tun da idan ba ka iya kama ɓarawo ba sai shi ya kama ka. Saboda har kawo lokacin ba a san musababbin mutuwar kajin ba. Shi kuma Lado abin da ya sa yake bin dare yana ɗaukar kaza ko zakara yana ba su guba bai wuce 'yan kuɗaɗen da Mami take ba shi ba, shi ya sa Uwani ta yi masa tambayar duniya ya nuna mata shi taimakonta dama yake yi da yake yankawa kafin su mutu amma tun da ba ta so shi kenan. Watarana kimanin ƙarfe biyun dare Lado ya fito cikin sanɗa ya nufi garken Uwani, don a wannan ranar Mami ta ba shi dubu biyar ta ce ya ɗauki ɗaya daga cikin awakin Uwani ya ba ta guba. Lado cikin sanɗa ya a jiye kofin da yake kaɗa shinkafar ɓeran a ciki, ya shiga cikin garke a lokacin awakin duk suna kwance. Lado na ɗagowa ya ga wani ɗan bunsuru ya ƙura masa ido yana kallo, Lado ya waiga hannu da dama sannan a hankali ya furta. "Wato kai don ubanka kallona kake yi ko? To alƙur'an yau kwananka zai ƙare, shege kana fama da ƙwala-ƙwalan ido kamar gurjiyar lahira." Lado na gama magana ya kai wa ɗan akuyan duka a kanda, sai kuma shi ma Lado ya ji kamar an shafo masa ƙeya ta baya, da sauri ya waiga amma bai ga kowa ba. Sunkuyawa ya yi ya cicciɓo ɗan bunsurun, ga mamakinsa ya ji shi da wani irin nauyi tamkar wanda ya ɗauki ƙatuwar tinkiya, Lado yana tafe yana nishi har zai fita daga cikin garke ya ji bunsurin ya ce. "Idan ka fitar da ni daga cikin garken nan kai ma sai ka ci ubanka Lado. Kuma ka sauke ni daga kanka ka ga idan za ka iya." Lado na jin haka ya fara fitsare wandonsa cikin tashin hankali, ya sunkuya zai sauke shi ya ji bunsurun ya manne da wuyansa. Dariya ya ji bunsurin ya saki ya ce, "Ai ni da kai mutu ka raba Ladodo." Bunsurun na gama magana ya zura hannu yana shafa ƙirjin Lado sai kuma ya ce, "Ni Lado ko haike maka zan yi ne ma tun da kai ka kawo kanka?" Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 First bank shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne 🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Wasu 'yan tagwayen ƙwalla ne suka zubo wa Lado jin abin da bunsurun ya faɗa, jiki na karkarwa ya furta. "Don Allah ka yi haƙuri ka yi mini rai ka rabu da ni. Wallahi ba zan sake taɓa ku ba." Bunsurun ya yi kasaƙe yana sauraronsa sannan ya kai hancinsa ya fara sunsunar gefen wuyan Lado, har zuwa wurin kunnuwansa sannan ya furta. "Ai na riga da na gama magana Ladodo, idan kuma ka bari na sauka daga bayanka waccen gubar da ita zan shayar da kai." Tashin hankalin da Lado ya shiga ne ya sa ƙafafuwansa suka yi masa sanyi, ya tsugunna a cikin garken awakin hawaye na zuba. Bunsurun ya sake sansano wuyan Lado sannan ya ce. "Lado ka yi auren fari kuwa? Don na ji ƙamshin samartaka kake yi" Lado ya fara girgiza kai yana hawaye, bunsurun ya zura ƙafarsa ta gaba cikin rigar Lado yana shafa ƙirjinsa, wani abu ya ji ya tsire shi kamar an caka masa allura, lokaci ɗaya ya ji ƙirjinsa ya yi nauyi ya kuma yi masa ƙababa. Lado na kai kallonsa sai gani ya yi mama ya cika masa ƙirji, ya ta ƙarƙare ya fasa ihu hankalinsa a yanzu har ya fi na kowanne lokaci tashi. Fuska cike da hawaye ya ce, "Na shiga uku an mayar da ni mata-maza, don Allah ka yi mini rai ka mayar fa ni yadda nake wayyo Allahna!" Sai a lokacin bunsurun ya sauka daga bayan Lado, ya fara tafiya yana kaɗa masa jela sannan ya ce. "Lado duk fa ihun da za ka yi babu mai jin ka, don haka idan ka na son na mayar da kai daidai sai ka kawo mini Saratu a daren gobe." Tun bai gama magana ba Lado ya fara gyaɗa kai ya ce, "Wallahi ko yau kake so na kawo ta zan kawo maka ita." Bunsurun kunnen Lado shafa da kofatonsa ya ce. "Ko mu mayar da kunnuwanka na giwa ne?" Da sauri Lado ya ce. "Don Allah ku bar ni haka wallahi wannan ma ban san ina zan kai ƙirjin nan ba." Bunsurun ya furta. "Ai ni da na dasa maka na san yadda zan yi da su, kai dai ka kawo ido ka sa ka gani ka ji Lado." Daga haka bunsurun ya tasa Lado a gaba ya saka shi tsallen kwaɗo, Lado yana yin tsallen kwaɗo bunsurun yana ranƙwala masa kofotonsa a fuska da kansa. Sai da Lado ya gama galabaita sannan ya nemi bunsurun sama da ƙasa ya rasa, shafo ƙirjinsa Lado ya yi ya ji yana nan kamar na mata ai kuwa ya rushe da kuka. Ga fuskarsa duk ta kumbure ta yi ja abin ka da farin mutum, saboda har marinsa bunsurin ya dinga yi da kofato. Ganin kukan ba zai kai Lado ba ya sa ya faɗa ɗakinsa ya haɗa kai da gwiwa, yana da-na-sanin zuwansa aiki gidan Daddy. Yanda Lado ya ga rana haka ya ƙarasa ganin darensa, sai da aka yi assalatu bayan gari ya yi haske sannan ya samu ya faɗa banɗaki ya ɗauro alwala ya yi sallah. Jingina ya yi da bango da ya kai kallo kan ƙirjinsa sai kawai ya ɓarke da kuka, tashi ya yi ya tuɓe rigar jikinsa ya ciro wata rigar sanyin sa ya saka sannan ya ɗauko wata rigar shadda ya ɗora a kai. Da yake lokacin zafi ne nan take ya fara sharɓa gumi, bai damu da gumin ba tun da ya samu ƙirjin ya rufe ba za ka fahimta ba idan ba ƙura masa ido ka yi ba. Tun da ya ga gari ya yi haske yake alla-alla Mami ta fito don ya san ƙaryar da zai yi mata, wacce za ta sa da daddare ya kai ta tirken Uwani. Ƙarfe shida daidai na safe Salim ya kira Mami hankali a tashe sakamakon rashin lafiyar da Shukra take fama da ita, da yake Daddy ba ya gari a gagguce Mami ta shirya sai da ta je bakin gate, sannan ta leƙa ɗakin Lado ta hango kwance yana kallon silin da alama ya lula duniyar tunani. Har Mami ta fice daga gidan Lado bai sani ba, kai tsaye Mami ta wuce asibitin Noor clinic inda aka kai Shukra. A lokacin da Mami ta je ta samu bacci, sai da suka gaisa da Salim ta fara tambayarsa abin da yake damunta. Salima sai da ya sosa kai sannan ya furta. "Dama ciwon ciki take yi Mami, sai ciwon ƙirji da yawan amai. To kuma yau sai muka tashi numfashinta na ɗaukewa." Salim ya sake sunne kai ƙasa yana shafa kai ya ce, "Likita kuma ya ce tana da juna biyu." Washe baki Mami ta yi ta furta. "Kai AlhamduLillah, na yi farincikin wannan labarin. Allah Ya raba lafiya " Mami zama ta yi sai bayan wani lokacin Shukra ta farka, aka haɗa mata ruwan shayi. Kaɗan ta sha saboda tashin zuciyar da take fama da shi, duk da a haka ma an yi mata allurar tsayar da amai. Ganin yanayin jikin Shukra ya yi kyau ya sa aka sallame ta, sai dai a nan take Mami ta kira Auta ta ce mata ta ba wa Uwani waya, saboda ita ko lambar Uwani babu a wayarta. Lokacin da Uwani ta karɓi wayar Mami ta ji ta furta. "Maza ki haɗi kayan sakawarki da uniform ɗin ki, Auta za ta rako ki gidan Shukra ba ta jin daɗi za ki dinga tayata aiki." Da yake har Aunty na zaune Mami ta faɗi haka, saroro Uwani ta yi. Yanayinta kawai Aunty ta kalla ta miƙa hannu ta karɓa ta ce. "Aunty Saratu ashe Shukra ce ba ta ji daɗi ba a wane asibitin kuke?" Mami ta saki guntun tsaki ta ce, "Da sauki." Aunty na shirin sake magana Mami ta katse kiran. Uwani ba don ta so ba Aunty ta sa ta haɗa kayanta, don ba ta son abin zai dinga haɗo ta Mami ballantana watarana ta yi mata sharri. Auta ma ta saka kayanta a jaka kamar yadda Uwani ta sa duk da Mami ba ta ce ita ma ta haɗa ba. Suka yi wa Aunty Sallama suka wuce can gidan Shukra. Lokacin da su Uwani suka ƙarasa gidan Shukra su Mami ba su jima da ƙarasawa ba, Shukra an yi ɗaiɗai sai juya idanu ake lokaci-lokaci ta tashi ta zubar da yawu. Su Uwani na shiga Mami ta shiga aikawa da Auta harara, ita kuma ta kawar da kanta kamar ba ta san abin da Mami take nufi. Saboda Salim yana wurin ya sa Mami ba ta yi magana ba, da mamaki Salim yake bin Uwani yana ganin kamar ya taɓa sanin fuskarta. Bayan da Salim ya fita ne Mami ta dubi Auta ta ce, "Ki taso mu wuce gida, kin san ba a garin gaɓa-gaɓa muke ba da za ku zo har ku biyu ku zaune mata a gida." Auta na shirin magana Mami ta buga mata tsawa babu musu Auta ta ɗauki jaka, suka fice ko sallama ba ta yi wa Shukra ba. Mami har ta yi wa Shukra sallama ta waiga wurin Uwani ta ce. "Kin ga dai halin da take ciki, ki tabbatar kina yi mata duk wani abin da ya dace. Idan ba haka ba ranki ne zai ɓaci, saura kuma ki dinga saka mata ido da waɗannan ƙwala-ƙwalan idanun na ki idan tana hira da mijinta." Uwani ta amsawa Mami sannan ta yi gaba. A hankali Uwani ke bin falon Shukra da kallo tun da dama ba ta taɓa zuwa gidan ba. "Wannan kalle-kallen ba zai ƙare miki ba tun da abin kallon yana da yawa a gidan nan, da alama babu a ɗakin gyatuma ne? Ki tashi ki je ɗakina akwai kayan da na ɓata ɗazu kafin mu je asibiti ki wanke su." Ƙurr Uwani ta yi tana kallon Shukra, sai da ta haɗiyi yawu mai ɗaci sannan ta furta. "Kin san shi dama arziƙi kashi ne taka shi ake Aunty Shukra, ni ban yi mamaki ba don babu a ɗakin mahaifiyata. Idan ban manta ba Dada ce mini ta yi da kuɗinta ta saya wa Mami samiru, wai ko iya kwanon silba aka kawo ta da su..." A hassale Shukra ta ɗago ta ce. "Don uwarki magana za ki faɗa mini?" Uwani ta saki murmushi sannan ta miƙe tsaye ta saɓi jakarta ta furta. "Kina buƙatar hutu Aunty Shukra kin san mai ciki ba ta buƙatar hayaniya, ni yanzu ina ne ɗakin da zan zauna na kai jakata?" Baƙin ciki ya mamaye zuciyar Shukra ganin Uwani na niyyar mayar da ita marar hankali, sai da ta yi ƙwafa ta ce. "Ga shi nan yana kallonki." Uwani ta ɗauki jakarta tana tafe tana kallon falon a yamutse sannan ta tura ƙofar ɗakin ta shiga, tana shiga wani zarnin fitsari ya doko hancinta. Ga dai ɗakin daga katifa sai ƙaramin mudubi da banɗaki, amma a mamakinta wanne irin zarni ne haka ita shukra da ba yara gare ta ba. Daga can wurin ƙofar banɗakin take jiyo warin na fitowa, ta sa hannu ta toshe hancinta ta tunkarin banɗakin. A yamutse ta dawo falo ta ce, "Aunty Shukra baƙi kika yi ne suka yi miki fitsarin kwance ne a ɗakin can?" Shukra ba ta tanka mata ba, ganin ba ta da niyyar tanka mata ya sa Uwani ta miƙe ta shiga ta sauya kaya, wata doguwar riga ta saka mara nauyi ta ɗora hula a kanta. Ɗakin Shukra ta shiga ta fara bin ɗakin da kallon mamaki a yamutse, saboda tsantsar shirgi da wari-warin da yake yi. Mami da Auta na zuwa gida Auta ta wuce ɗakinta cikin fushi, Mami har ta gota ɗakin Lado sai ta dawo tana bin garken Uwani da kallon tsana. Ƙwanƙwasa ƙofarsa ta yi, a sanyaye Lado ya amsa yana zuro kai ta windo. Ganin Mami ya sa ya saki ajiyar zuciya ya ɗan washe baki. "Hajiya barka da shigowa." Da ido take bin lado ganin wata irin rama da ya yi lokaci ɗaya don ko jiya da ta gan shi bai zuge haka ba, malolon fuskarsa ta kalla ta ce. "Lado me ya faru da kai haka? Na ga fuskarka duk a daddauje yau kuwa ka ma ci abinci kuwa?" Lado sai da ya saci kallon ƙirjinsa don kada Mami ta fahimci halin da yake ciki ya wayance da cewar. "Hajiya abin duniya ne ya ishe ni." Lado ya ɗan waiga yana hange-hange zai yi magana Mami ta ce. "Ban gane abin duniya ne ya ishe ka ba, shi ya sa duk ka yi zumu-zumu kamar zakaran mayu?" Lado ya yi ƙasa da murya ya ci gaba. "Hajiya a kanki ne fa abin yake shirin faruwa, dama ɗazu ma na so yi miki magana sai jin fitarki kawai na yi. Dalilin da ya sa ma jiya na kasa kashe ɗaya daga cikin awakin yarinyar can Uwani kenan." Mami cikin damuwa ta ce. "Ina jin ka Lado ci gaba." "Hajiya jiya cikin dare na fita ina cikin garken Uwani na hango wata kamar Aunty wato kishiyarki, a can ta tsaya babu kaya tana ambatar sunanki tana wanka da wani irin ruwa. Hankalina ya tashi sosai Hajiya shi ya sa na gagara sukuni kin gan ni yau ko abinci ban ci ba, ni dai yanzu ki zo da daddare wurin biyu daren ki gane wa idonki don na ji ta ce aikin na kwana uku za ta yi. Kin ga sai a tona mata asiri a gaban kowa." Lado ya ƙarasa maganar yana nazartar Mami, ajiyar zuciya ta sauke ta furta. "Kuma fa ka yi magana Lado, dama yau Daddyn yara zai dawo. Amma Abuwa an yi tsinanniya ni za ta sabauta? Yanzu Lado me na tsare mata a gidan nan?" Lado ya ɗan waiga don gudun kada wani ya ji zancen da suke yi asirinsa ya tonu ya ce, "Hajiya ki yi ƙasa-ƙasa kada ta ji ta gane shirinmu." Mami ta gyaɗa kai sannan ta ce. "Ita ma waccan shegiyar yarinyar dole ta daina wannan kiwon, ka tabbatar ka ƙara sayo shinkafar ɓeran nan." Lado ya jinjina kai sannan Mami ta wuce sashenta jiki a sanyaye, lokacin da ta shiga falo Aunty na zauna. Aunty na ganinta ta shiga tambayarta me jiki amma Mami ko ƙurarta ba ta kalla ba. Uwani zagewa ta yi sosai ta hau yin gyaran ɗakin Shukra, ba ƙaramar jinjina wa Shukra ta yi a ɓangaren ƙazanta ba. Kayan wanki ma sai da ta ɗaure ya kai ƙulli uku, bayan ta gama ɗakin Shukra ta koma ɗakin da ta ajiye jakarta nan ma ta hau gyara shi sannan ta koma kitchen. Kwanukan da ta gani busassu har da waɗanda idan aka ce sun kusa sati a haka ba za a musa ba, sai da Uwani ta jiƙa su sannan ta wanke su suka fita. Uwani na gama gyarawa ta kunna turaren wuta Shukra na kwance tana kallonta, lokaci ɗaya gidan ta ɗauki ƙamshi ita kanta Shukra yanayin ya birge ta. Bayan ta gama a wahalce ta faɗa kan kujera ta ce, "Me za a dafa Aunty Shukra?" A yatsine Shukra ta dube ta. "Ki je ki ɗebi shinkafa ki dafa daidai ke, ni dama ba girki nake ba Baby zai taho mana da abinci." Uwani ta kalli Shukra kamar ta tanka mata sai kuma ta tashi, firji ta buɗe ta ɗebo kayan miya ta ɗan jajjaga sannan ta yi miyar jajjage da farar shinkafa. Cikin galabaita Uwani ta sake zama za ta ci abinci Shukra ta furta. "Kin wanke mini kayan ne da za ki zauna cin abinci? Wai ko kin ɗauka ci ne ya kawo ki? Aiki kika zo yi mini yarinya sai kin gama komai za ki zauna." Uwani ta dafe kanta da ke yi mata ciwo ta ce. "Wallahi na gaji yau ba zan iya wanki ba sai gobe." Shukra ba ta tanka mata ba ta tashi ta nufo ta, a tunanin Uwani ko Shukra marinta za ta yi don haka ta ɗan ja baya. Shukra na zuwa ta ɗauki shinkafar gaban Uwani ta juye mata ita a kanta, sannan ta kai mata mari tana faɗin. "Don uwarki ni sa'arki ce da za ki faɗa mini haka? Ko Jidda kin isa ki faɗa mata haka ballantana ni? Kada ki gan ni ban da lafiya wallahi kika ƙure ni naɗa miki na jaki zan yi." Shigowar Salim kenan ya ƙarasa ya rungumo Shukra jikinsa yana faɗin, "Baby lafiya kike hayaniya haka? Kin manta abin da likita ya faɗa ne?" Tsaki Shukra ta yi ta ce. "Wannan jakar yarinyar ce ta ɓata mini rai, na ce ta wanke mini kayan sawa da wanda na ɓata tun ɗazu ta tsaya iskanci." Salim ya dubi Uwani a yamutse ya furta. "Ke dama Mami ba ta faɗa miki aikin da za ki yi ba ne? Baby ko ba mai aikinku da Mami ta ce za turo ba ce?" Kalaman Salim suka ɓata ran Uwani da wulaƙancin da Shukra ta yi mata, ta sa hannu a hankali tana karkaɗe shinkafar jikinta. Takaici ɗaya yunwar da take ji ga kuma iya shinkafar farantin kaɗai ta dafa, ta riski muryar Shukra na faɗin. "Ita ce mana, kasan ɗan ƙauye bai iya wayewa ba ai. Ba ta ga ta goge tana sa suturu masu kyau ba." Salim ya sake tallafo Shukra ya furta. "Ke gargaɗi zan yi miki, wallahi likita ya kafa wa matata dokoki domin samun lafiyarta da ta abin da ke cikinta. Idan har ta samu matsala ta sanadinki wallahi sai na ɗauki mummunan mataki a kanki, farin cikin Shukra shi ne nawa. Don haka duk abin da take so shi za ki yi mata." Daga haka Salim ya ja Shukra suka shige ɗaki, a ransa yana yaba kyawun gidan da ƙamshin da ke tashi don rabon da ya ga gidan ya yi kyau haka har ya manta. Uwani bayansu ta bi da kallo a hankali ta furta. "Ashe kuwa zan gyara muku zama ɗaya bayan ɗaya." Sai da Uwani ta gyara wurin sannan ta ɗebo kayan wankin Shukra ta fita gate ta fara wankewa, ba ita ta kammala wankin ba sai kusan sha ɗaya da rabi na dare. A galabaice ta koma ciki ta samu Shukra da Salim suna cin chips da ruwan tea, kitchen ta wuce ta ɓararraka taliya ta zuba ta wuce ɗaki ba tare da ta tanka musu ba. Daddy sai da ya dawo Mami take sanar da shi rashin lafiyar Shukra, amma sai ta nuna masa Uwani da kanta ce ta ce za ta je ta taya Shukra aiki. Don kada Daddy ya yi faɗa sai Mami ta ce masa Salim ma baya gari, da ya samu Aunty da maganar tafiyar Uwani jin abin da Mami ta faɗa ya sa ta ja bakinta ta yi shiru, don wani abin ba ta so ta fiye shigewa tun da ta lura Mami mace ce mai makirci. Kamar yadda Lado ya tsara wa Mami hakan ce ta kasance, ƙarfe biyun dare na yi ta fito a hankali kai tsaye ta nufi wurin garken Uwani. Da yake Lado a matse yake da ya samu a raba shi da ƙirjin jikinsa tun ƙarfe ɗayan dare yake duba agogo bai ji motsin Mami ba. Cikin garke ya sa ta suka shiga a hankali ta ce, "Lado ya ban ganta ba." Lado na shirin yin magana Mami ta ji an ɗane mata baya, ta waiga a firgice za ta yi ihu ta hangi bunsuru a saman kanta ya ce. "Duk ihun da za ki yi a yanzu babu mai jin ki." Ganin bunsuru na magana ya sa Mami ta saki fitsari ƙafafuwanta na karkarwa. Bunsurin ya dira kan katangar da ke zagaye da garken ya nuna Mami da kofatonsa ya ce. "Wato ke ce kike aiko Lado domin ya tarwatse kiwon Uwani ko?" Mami jiki na rawa ta ce. "Ba ni ba ce..." Taass ta ji saukar mari a kuncinta, nan take ta yi shiru tana hawaye. Bunsurun ya zayyane mata duk abin da ya faru tsakaninsa da Lado. Wani irin tsoro ne ya mamaye ta, nadama da da-na-sani suka shige ta. Sannan bunsurun ya ɗora da cewa. "Kowannenku akwai hukuncin da zan yi masa, kuma na fara da kai Lado ka ga na ka sakamakon saura ke." Lado zai yi magana ya ji bakinsa ya yi ɓam tamkar an danne shi da dutse, bunsurun ya ƙarasa ya fisge ɗankwalin kan Mami. Tana son ta motsa abu ya gagara, bakinsa ya sa ya hura kan Mami nan take ta ji wata iska na shiga kanta. Ya sauka daga kanta ya ce. "Kuma idan kika kuskura kika bari Uwani ta dawo gidan nan sai na ba ki mamaki, don haka duk wani makirci da za ki yi don ta zauna a can gidan ki yi shi har sai na ba ki wa'adin dawowarta. Idan kuwa ta dawo gidan nan za ki yi kuka da idonki, ba dai so kike ta tafi can gidan Shukra ba? Yanzu ta fara zaman gidan, ku kuma yanzu za ku fara girbe abin da kuka shuka." Bunsurun na gama magana suka ga ya ɓace, ɓacewarsa ta yi daidai ta sulluɓowar gashin kan Mami gabaɗaya. Mami ba ta ankara ba sai ji ta yi kanta ya yi ƙwaryar molo babu ko ɗigon gashi, ta baya ta ji an shafo ƙeyarta a guje ta fice daga cikin garken. Lado kafin ya kai ɗakinsa sai da ya yi faɗuwa kusan uku. Littafin kuɗi ne a kan 500 ta wannan Acc Aisha Adam 3090957579 First bank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Mami saboda firgici da tashin hankali tana gudu tana dungurawa har ta shige cikin ɗakinta, tana shiga ta ji cikinta ya hautsina mata da rarrafe ta shiga banɗakin tun ba ta ƙarasa ba gudawa ta fara bin ƙafarta. Mami tana sakin gudawa tana kukan tashin hankali, a haka har ta gama ta cire kayanta ta gyara wurin. Kamar kazar da aka tsamo daga ruwa haka Mami ta faɗa kan gado yaraf, ta shafo kanta sai jin sa ta yi ya koma kamar bayan sulba. A haka gari ya wayewa Mami kafin asuba ta shiga banɗaki ya fi sau biyar, ko da gari ya waye jin ta shiru babu motsi ya sa Daddy ya leƙa ɗakinta. A kwance Daddy ya hango ta ta yi ringingine da alama ta lula duniyar tunani ba ta ji motsin shigowarsa ba. Sai da gari ya yi haske ta fahimci duk wata kafar gashi ta jikinta ta siɗe tamkar ba a taɓa tsirar gashi a jikinta ba, babban abin da ya fi ɗaga mata hankali bai wuce yadda ta ga gashin gira da na idonta sun siɗe fuskarta ta yi fayau ga goshin da kanta sun yi sanƙwalƙwal ba. Da mamaki Daddy yake bin ta da kallo ya furta, "Saratu!" Jin kiran da Daddy ya yi mata ya sa Mami ta tashi a zabure tana kokawar rufe kanta. "Me nake gani haka a kanki Saratu?" Daddy ya jefa mata tambaya cike da mamaki. Idanun Mami suka ciko da ƙwalla amma da yake tsoro ya mamaye ta sai ta tattaro murmushin yaƙe ta ce. "Daddyn yara ai aski na yi jiya, wallahi kan ne ƙuraje ya takura mini. Gobe ma nake son ɗaukar azumi sai na yi ukuna a jere na huta." Daddy sake da baki yake bin Mami da kallo, don rabon da ya ga murmushinta har ya manta. Ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Saratu askin ne har da saman idonki kika kwashe? Me ya kai ki aske gira alhalin kin san bai dace ba?" Mami ta haɗiyi yawu mai ɗaci ta ce, "Tsautsayi ne, da yake mai ne na fara gwada shi a gira ta na ga ko yana da kyau, ina wankewa na ga ya kwashe mini gashi." Shiru Daddy ya yi yana dubanta, alamunsa ya nuna rashin gamsuwa da zancenta. "Allah Ya kyauta! Sai ki yi ta Istigifari kuma nan gaba kada ki sake wannan gangancin." Daddy ya furta yana fita daga ɗakin. Mami na ganin Daddy ya fita ta kife a kan gadon ta rushe da wani irin kuka, da yake Daddy bai yi nisa ba jin gunjin kuka ta ya sa ya sake turo ƙofar. A zabure Mami ta tashi zaune tana goge hawaye, Daddy ya yi mata kallon tsaf ya ce. "Saratu an ya babu abin da yake damunki kuwa? Kukan me na ji kina yi." Mami ta rasa ƙaryar da za ta yi wa Daddy tun da ga hawaye nan shaɓe-shaɓe a fuskarta, don haka ta ce. "Kuka nake saboda saɓon da na yi wa Ubangiji, don Allah Daddyn yara ka ta ya ni addu'ar Allah Ya yafe mini kuskuren da na aikata." A wannan karon ma Daddy kallonta ya yi cike da tuhuma, ya jinjina kai sannan ya fice daga ɗakin. Lado na zaune a cikin ɗakinsa daga shi sai singlet yana shan iska saboda zafi sai ya ji bugun ƙofa, tun da wannan al'amarin ya same shi ya daina kwanciya shan iska a gate. Bugun da ake yi da ƙarfi tamkar za a ɓalle ƙofar ce ya razana shi, a guje ya fita ya zare sakatar yana faɗin. "Wai waye haka ne ana zuwa!" Cikin gajiya da bugun ƙofar Dada ta ce. "Uwar Mamman ce, Lado ko iyaka za ka yi mini da ganin ɗana?" Lado ya shafa kai yana murmushin yaƙe ya ce. "Ni na isa Dada!" Lado ya yi maganar yana russsunawa ƙasa ya furta. "Ina kwana Dada." Karaf idanun Dada suka sauka a kan ƙijin Lado, da sauri Dada ta ja baya tana dafe ƙirji, ita dai a iya saninta da Lado ba ta taɓa ganin wannan sabuwar hallitar a jikinsa ba. Ta sha zuwa ta same shi babu riga yana wankin motar Daddy, amma ba ta taɓa ganin haka ba. "Ko dai gamo na yi?" Dada ta raya a ranta, a tunanin Lado ko Dada ba ta ji shi ba sai ya sake cewa. "Ina kwana Dada?" Da sauri Dada ta yi ciki tana faɗin, "Lafiya ƙalau Lado ai tuni na amsa maka." Ta ci gaba da sauri kamar za ta tashi sama, Dada tana tafe tana waige. Lado sai a lokacin ya fahimci saurin da Dada take yi, cike da faɗuwar gaba ya shige ɗaki jin Baba Mustafa ya turo ƙofar yana sallama. Rigar sanyin da Lado ya saba sakawa ita ya mayar sannan ya leƙo yana dariyar yaƙe ya gaida baba Mustafa. Kamar wacce aka biyo da gudu haka Dada ta faɗa falon cikin sauri, Daddy da Aunty suna zaune suna hira suka ji sallamar Dada. Da murna suka tarbe ta Daddy ya ce. "A'a Dada yau ke ce a gidan sannu da zuwa." Dada jiki a sanyaye ta ce, "Ɗan uwanka Muɗɗafa ne ya kawo ni, yana can ƙofar gida." Daddy ya ce, "Au me makon ya shigo kuma." Daddy har ya nufi hanyar fita Dada ta ce. "Mamman dawo ka zauna!" Ganin yanayin sanyin jikin Dada ya sa Daddy ya dawo a sanyaye, musamman da ya tuna ko waya ba ta yi masa ta ce za ta zo ba. Don ɗabi'ar Dada ce ba ta zuwa sai ta kira shi. "Mamman ni dama mutum yana zama mata-maza da girmansa kuwa?" Daddy ya yi jim sannan ya ce. "An ya kuwa Dada? Duk da dai ba ɓangarena ba ne amma ba na jin haka za ta faru, matuƙar dai mutum da girmansa ne." Dada ta zuba hannuwa biyu ta yi tagumi a fili ta ce. "To ko gamo na yi ne Mamman?" "Gamo kuma Dada?" "Alƙur'an yadda na ga Lado da ƙirjin mata Allah Ya nuna mini Annabi. Idan kuwa haka ne ni dai gamona yi, Allah Ya sani Mamman gidanka nema yake ya fi ƙarfinka yanzu." Dada ta ƙarasa maganar tana hawaye. "Ni dai a iya sanina da Lado ba shi da wata hallitar mata Dada, kin manta Lado fa tun bai fi shekara goma sha biyar yake yi mana gadi." Dada ta miƙe tana share ƙwalla ta furta. "To ni dai Saratu ta janyo wa zuri'ata masifa." A daidai lokacin Mami ta fito an sha ɗaurin ɗankwali an yi shar, Mami ta ɗan saki fuska ta gaida Dada. Saboda tun abin da ya faru tsakaninta da bunsurun nan wani irin tsoro ya shiga ranta, take tsoron kada ta yi wani abin a wani daren ta sake gamuwa da gamonta. Dada na shirin amsa gaisuwar Mami sai gani suka yi an fisgi ɗankwalin kan Mami an yi wurgi da shi, gaba ɗaya mutanen wurin babu wanda bai lura da abin da ya faru ba. Dada da Aunty suka saki baki cikin mamaki. "Saratu mene ne haka?" Dada ta tambayi Mami tana ja da baya, Mami ta yi murmushin yaƙe sannan ta yi wa Dada bayanin da ta yi wa Daddy. Dada gaba ta yi tana jinjina kai ta ce, "Mamman ni kam Allah ya ba mu alheri, gaskiya ina da abin yi a gida." Duk yadda Daddy ya so Dada ta haƙura ko zuwa yamma ne ta kai fir ta ƙi amincewa. Tun bayan da Lado ya gaisa da baba Mamman ya fara jin kukan 'ya'yan akuya a cikin kunnensa, waige ya fara saboda a kunnensa yake jin yadda suke tsalle da dire-dire a harabar gidan. Ganin baba Mustafa na tsaye yana danna wayarsa ya fahimci shi kaɗai yake jin wannan kukan awakin. Yana nan tsaye ya hangi su Dada sun fito, daga gefensa ya ji an taɓo shi yana waigowa ya ga bunsurun nan a gefensa ya ce. "Ya'yana suna jin yunwa don haka za su zo su sha." Jin haka ya sa Lado ya fashe da kuka ya ce, "Don Allah ka yi haƙuri, yau ni na zama uwar bunsurai kenan?." Baba Mustafa ya kalli Lado da mamaki ganin yana magana shi kaɗai kuma yana kuka shaɓe-shaɓe. Yana shirin yin magana sai ji suka yi Lado ya zabura yana fisgar riga yana faɗin. "Jama'a ku taimaka mini bunsuru zai danne ni! Wayyo ƙirjini, ya fara kiciniyar shayar da su." Da sauri Baba Mustafa ya matsa wurin Lado, a lokacin Daddy ya ƙarasa. Kici-kici haka Lado ya fara kokawa da bunsurin har ya kwayewa Lado riga, hannuwa biyu Lado ya sa ya dafe ƙirjinsa yana nan kwance ya hango wasu ƙananan bunsurai biyu sun yo kansa. Da ƙarfi 'ya'yan bunsuran suka bankaɗe hannuwan Lado suka kafa bakinsu a jikinsa. Lado na jin haka take numfashinsa ya ɗauke, yaraf ya faɗi a ƙasa sumamme. Mamaki ne ƙarara ya bayyana a fuskokinsu, Dada ta riƙo hannun Daddy cike da tsoro ta ce, "Mamman ka ga abin da nake nuna maka, wai ka lura da Lado ko idanuna ne?" Daddy ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Na gani Dada, amma ban taɓa ganin haka a tattare da shi ba." Baba Mustafa ne ya ɗauki butar Lado da ke gefe ya yayyafa masa ruwa, a zabure Lado ya miƙe yana dafe ƙirji yana faɗin. "Zuƙata suke yi, wallahi ga su nan suna zuƙe ni. Wayyo ƙirjina 'ya'yan bunsurai suna zuƙe ni..." Daddy ya riƙe hannuwansa yana tofa masa addu'a, a hankali Lado ya dawo cikin nutsuwarsa ya fara bin su da kallo. Ya sauke kansa yana kallon ƙirjinsa sai kawai ya fashe da kuka ya ce. "Daddy dubi ƙirjina, ni kam na saddaƙar rayuwata ta zo ƙarshe. Wai yau ni ne bunsurai suke tsotsa, Daddy me ya rage ni ma ai na zama bunsuru." Cikin tasuyawa Daddy ya ce. "Me ya faru Lado, gaya mini." Jim Lado ya yi ya ce, "Zan faɗa maka komai, wallahi duk abin nan da ya faru da mu daga ni har Mami ita ce sila. Hajiya ta cuce ni ta cuci rayuwata, wallahi ita ta kai ni ga halaka. Don Allah ku kira mini Uwani na nemi yafiyarta." Shiru duka suka yi suna mamakin kalaman Lado, Daddy ya ciro waya ya kira Malam mai Baƙara ya ce masa yana son ganinsa akwai aikin gaggawa da zai gudanar. "Kai Lado, dube ni nan. Ka faɗa mini me ka shuka wa Uwani kai da Saratu da na ji kana neman yafiyarta?" Dada ta furta tana tsare shi da ido. Lado ya share ƙwalla ya ce. "Hajiya ce ta sa nake kashe kaji da zakarun Uwani da suke mutuwa, ta yi mini barazanar za ta sa a kore ni daga aiki idan ban aikata ba." Lokaci ɗaya su Daddy suka ɗauki salati. Kiran sallar asuba a kunnen Uwani aka yi saboda tsabar ciwon jiki ko baccin kirki ba ta yi ba, bayan ta yi sallah ta yi azkar ta kwanta a gefen katifa nan take bacci ya yi awon gaba da ita. Sai a wannan lokacin Uwani ta samu bacci mai daɗi, tana cikin bacci sai ji ta yi an sheƙa mata ruwan sanyi a kanta. A firgice ta tashi tana dube-dube, Shukra da ke sanye da wata figigiyar rigar barci ta ce. "Wai Uwani ke wacce irin daƙiƙiya mai ƙwaƙwalwar kifi ce? Ina ce jiya na faɗa miki aiki kika zo ba hutu ba?" Ran Uwani ba ƙaramin ɓaci ya yi ba ta ce. "Amma me ya sa ba za ki iya tashina da hannunki ba har sai kin sheƙa mini ruwa?" Shukra ta matsa gaban Uwani cikin isa ta ce, "Zo ki rama, na ce ki zo ki rama idan ban karairaya ki ba." Uwani ta yi ƙwafa ba tare da ta tanka mata, don ta ɗaga mata ƙafa ne saboda cikin da ke jikinta. A yadda ta fusata gani take idan ta rufe ta da duka mai ƙwatarta sai Allah. Fita Uwani ta yi ta ɗauko moper ta goge wurin, ta saka wani ɗan kwalin kayanta ta tsane ruwan kan katifar sannan ta nufi kitchen. Tana cikin kitchen ta ji fitowar Salim, saboda takaici da ya leƙa kitchen ɗin ko ƙurarsa ba ta kalla ba. "Uwani ba ki ga Baby ba, ba shi da arziƙin da za ki gaida shi ne.?" Shukra ta furta a gadarance. "Aiki ne ya kawo ni ba gaisuwa ba." Uwani ta faɗa fuska a haɗe, ta ci gaba da tattara kayan kitchen ɗin duk da gidan ba wani datti ya yi ba. Shukra ta riƙe baki ganin Uwani ta yarfa ta a gaban Salim, Salim ya jinjina kai ya ce. "Baby wannan mai aikin Mamin lallai tana haƙuri da ita, har ta samu sukunin faɗa wa 'yan gida magana?" Shukra ta yi ƙwafa za ta yi magana Uwani ta katse ta da cewar. "Me zan dafa da safe ko yanzun ma Baby ne yake sayo muku abin breakfast?" Shukra ta jinjina kai ranta na suya ta ce, "Tuwo nake sha'awa da miyar agushi..." "Ba zan iya tuwo a farar safiyar nan ba saboda ina da school ƙarfe takwas." Uwani ta katse Shukra sannan ta ɗora da cewa. "Ki faɗa mini abin da zan iya sarrafawa kafin na fita, idan ba haka ba zan haɗa iya cikina." Shukra sororo ta yi tana kallon Uwani don yanzu ba ƙaramin mamaki take ba ta ba. Miƙewa Shukra ta yi ta naɗe hijabin da ta sako ta nufi wurin da Uwani ke tsaye, ba ta tanka mata ba kawai ta ɗauke fuskarta da mari. Uwani ta dafe gefen kumatunta tana shirin yin magana Shukra ta sauke mata wani marin a ɗayan kumatun ta ce. "Kafin ki bar gidan nan sai na sauke miki iskancin da ke kanki..." Taaasss Uwani ta ɗauke kumatun Shukra da mari wanda ya yi sanadiyar maƙalewar maganar da take yi, Shukra ta saki baki tana kallon Uwani ba ta yi aune ba ta ji Uwani ta sake ɗauke fuskarta da mari. A fusace Salim ya ƙarasa ya ɗauke Uwani da wani azababban mari, Uwani ta yi gefe Salim ya fisgi wata wayar caja a gefe ya shiga zabga mata da ƙarfi. Sosai Uwani take jin dukan na shigarta, ganin ba shi da niyyar daina dukanta ya sa ta ƙwalla wata irin ƙara sai kuma ta faɗi ƙasa yarafff. Kallon juna suka shiga yi tsakanin Shukra da Salim, a tsorace Salim ya ce. "Ko suma ta yi?" Idanun Shukra suka ciko da ƙwalla ta ce, "Idan Uwani ta mutu a gidan nan na shiga uku, wallahi babu abin da zai hana Daddy bai maka ni a wurin hukuma ba." Uwani ta yi fakare tana sauraronsu, Salim da ƙirjinsa ke bugawa ya ce. "Ba kin ce 'yar aiki ba ce?" Shukra da hawaye bibbiyu ya fara zuba ta ce. "Wallahi ba 'yar aiki ba ce matar Ya Jafar ce, cousin sister ɗina ce." A razane Salim ya ce. "Matar Ya Jafar fa?" Shukra ta ƙara gyaɗa kai hankali a tashe, wata irin dariya suka ji Uwani ta ƙyaƙyace da ita Sai kuma ta miƙe tsaye tana ƙwanbare hannuwa tana zare idanu. Salim ne ya fara ja da baya ita ma Shukra ta fara matsawa a tsorace har suka fito falo, da ƙarfi Uwani ta fisgo labulen falon ta yi wurin su Salim ta hau ranƙwala musu ƙarfen labule. Sai kuma ta wurgar da shi ta fara tafiya da baya-baya ta ce. "Yau kun shiga dubu ɗari uku, domin kun tsokalo wa kanku tsuliyar dodo. Kun taɓo mana Hakima dole a yi muku babban hukunci. Salim da tuni jikinsa yake karkawa ya ce. "Don Allah ku yi haƙuri wallahi tsautsayi ne." Uwani ta waiga da sauri tana zaro ido waje ta nuna shi da yatsa ta ce, "Tun da kai ka fara magana ya zama wajibi mu fara hukunta ka. Hukuzufu fisge masa ƙafa ɗaya ka wurga wa Shugabar mayun fararen aljanu ta cinye." Jin haka ya sa Salim ya buga ihu ya tsallako gaban Uwani ba tare da ya sani ba. Uwani ta fakaici Salim ta ranƙwala masa cokali a kansa, cikin azaba ya fasa kuka ganin haka Uwani ta faɗa kitchen ta ɗauko robar yaji. Tana fitowa ta ga suna rige-rige za su shiga ɗaki, da sauri Uwani ta ce. "Idan kun shiga ma ba ɓuya kuka yi ba Ɗan bulluƙutu yana nan yana jiranku, shi da ma sare gaɓoɓin jiki yake yi." Cak suka tsaya, Shukra na kuka ta ce. "Don Allah ku yi mana rai wallahi ba za mu sake taɓa ta ba." Uwani ba ta kula ta ba ta miƙa wa Salim robar yajin da cokali ta ce. "Ɗan guzum ya ce ka sha cokali goma idan ba haka ba kuma zai gwagwaɗa maka, wato ya yi maka tsarki da shi." Salima yana ji yana gani ya ɗebi cokali ɗaya ya tura a baki, ai kuwa sai ga ido, hanci da baki na zuba. Cikin hawaye ya tsugunna a gaban Uwani ya ce, "Don girman Allah ku yi haƙuri mun yi nadama." Uwani ta tafi da gudu ta danne kusurwar bango tana faɗin, "A'a 'yar fincin kada ki fito, ki taimaka ki yi haƙuri wannan naman da kika samu a sannu za ki gana da shi, amma ki bari mai girma ya gama hukunta su." Ta wurga wa Salim wani kallo take ya sake dumbuzar yajin da cokalin ya cusa a baki. Lokaci ɗaya Salim ya ɓarke da kuka ya ce. "Wallahi ni kam Shukra kin cuce ni." Shukra za ta yi magana Uwani ta ce. "Za ka yi wa matarka mari ashirin ƙwarara idan kuma ba za ka yi mata ba za mu sa aljanin da ya fi mu girman hannu ya yi mata saba'in." Jin haka ya sa Shukra ta ƙarasa gaban Salim ta ce, "Don Allah ku bari shi ya yi mini da kansa." Salim ya dubi fuskar Shukra, sai da ya lailayata da hannunsa ya share hawaye ya ce. "Baby zan mare ki ne ba don ina so ba. Kin san soyayyar da nake yi miki ba zan iya marinki ba sai da dalili..." Maganar Salim ta katse sakamakon wani gigitaccan mari da Uwani ta zabga musu daga shi har Shukra da hannuwanta. A gigice kusan lokaci ɗaya suka ƙwalla ƙara, Shukra ta faɗa ɗaki a guje Salim ya bi ta yana buga ƙofar amma ba ta bi ta kansa ba ta banka sakata. Salim yana kuka yana buga ƙofa har Uwani ta ƙarasa wurinsa, a lokacin hannunta ɗauke yake ta ludayin sulba. Da yake Salim ya gama tsorata hannu ɗaya Uwani ta saka ta fisgo rigar shaddarsa, sai ji kake ƙuuuum ta yi wurgi da shi. A zabure Salim ya miƙe yana ihu ya faɗa ɗakin da Uwani ta kwana shi ma ya banke ƙofar da sakata. Littafin kuɗi ne a kan 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 idan littafi ya kammala cmplt 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Uwani na ganin Salim ya shige ɗakin ta je ƙofar ɗakin da Shukra ta shiga ta fara bugawa, ta kausashe murya ta fara faɗin. "Wallahi sai mun yi maganinku, ke da mijinki kun tsokano bala'i mara yankewa. Idan ma ba ku buɗe ƙofar ba za mu ɗaga gidan gabaɗaya mu kifar da shi." Jin abin da Uwani ta faɗa ya sa Salim da Shukra suka sake shiga tashin hankali, Shukra ban da kuka babu abin da take yi. Ga shi babban tashin hankalinta wayarta na falo ballantana ta kira Mami ta sanar da ita abin da yake faruwa. Salim na cikin ɗakinsa ya laluba wayarsa ya ciro daga aljihu, lambar Saminu abokinsa ya kira cikin ƙasa da murya ya ce. "Saminu muna cikin tashin hankali." Saminu jin muryar Salim ƙasa-ƙasa ya sa ya ce. "Me ya faru abokina ka ɗaga murya ba na jin ka." Uwani na daga falo ta jiyo maganar Salim ƙasa-ƙasa don haka ta fahimci waya yake yi, da ƙarfi ta doka ƙofar ta ce. "Da kai da wanda kuke wayar sai mun haɗa ku mun murɗe muku wuya." Jin haka ya sa Salim ya fashe da kuka jiki na karkarwa ya sanarwa Saminu abin da yake faruwa, Saminu ya yi murmushin takaici ya ce. "Amma wallahi abokina ka ji kunya, yanzu aljanun yarinya ƙarama ne za su sa gotai-gotai da kai ka dinga kuka har ka rufe kanka a ɗaki, bari dama ta hanyarku zan wuce gani nan zan biyo." Duk maganar da suka yi Uwani na daga falo tana jin Salim har ya gama waya, shiru ta yi tana nazari a ɓangare ɗaya gabanta na ɗan faɗuwa don tana tsoron kada asirinta ya tonu a gane ba aljanun gaske ba ne. Uwani na daga tsaye ta hangi Shukra ta fara buɗe ƙofa tana zuro kai, da gudu Uwani ta nufi ƙofar tana faɗin. "Za mu ƙwaƙwale ƙwayar idonta." A guje Shukra ta sake danno ƙofar sai ta sake fashewa da kuka. Uwani tana nan a zaune babu jimawa ta ji Gali mai gadi ya wangale gate, wanda hakan ne ya ba ta tabbacin Saminu abokin Salim ne ya ƙaraso. Cikin kitchen ta shiga ta turo ƙofa ta yi luf, ba a daɗe ba ta ji sallamarsa cikin falon. Shiru Uwani ta yi ba ta tanka masa ba, a can ƙasa-ƙasa ta ji muryar Salim ya amsa. "Kai dallah matsoraci ka fito, wannan ma ai babban abin kunya ne ace yarinya ƙarama tana raina muku hankali. Ni akwai aljanin da zai ɗaga mini lissafi, ai ko ifiritu ne a kanta take masa wuya zan yi." Jin irin kurantawar da Saminu yake wa kansa ya sa Salim ya yi ta maza ya leƙo kai, ya yi ƙasa da murya yana faɗin. "Saminu ka yi ƙasa-ƙasa wallahi aljanun jikin yarinyar nan ƙarfi gare su." Saminu ya saki tsaki, ya ce. "Ubansu! Kai matsa gefe wai ina Shukran take ne ko ita ma ta shige ɗakin?" Sai a lokacin Shukra ta fito fuska a kumbure ta yi jawur, gefen kumatunta na hagu har da shatin hannun Uwani. "Salim tun da na samu Saminu ya fito wallahi gidanmu zan tafi." Shukra ta yi maganar tana ƙoƙarin fita. Daga cikin kitchen suka ji Uwani ta tuntsire da dariya, sai kuma ta fara wani irin gurnani. Salim da Shukra a zabure suka miƙe suna kallon juna, Saminu ya miƙe tsaye yana ƙwambare kafaɗu sai da ya zuba hannu a aljihu sannan ya ce. "Wannan fa kada ya dame ku, ku dai ku bar mini komai a hannuna. Ke wane ɗan iskan ne a kanki?" Saminu ya tambaya yana kallon ƙofar kitchen. Suna nan a tsaye carko-carko suka ga Uwani ta fito zuwa ƙofar kitchen ɗin ta tsaya, kanta ɗauke da ƙaton kwandon wanke-wanke. Gwalo ido waje ta fara tana wani harare-harare, sannan ta fara ɗaukan kwanukan ciki ta jifansu tamkar yadda ake jifan shaiɗan. Sai da Uwani ta ƙarar da kwanunka sannan ta tunkari Saminu da ke tsaye, ganin haka ya sa gaban Saminu ya faɗi amma sai ya dake don kada Uwani ta fahimci ya fara tsorata da lamarinta. Su Salim na ganin haka suka fara ja da baya, Uwani na zuwa ta kifa kwandon wanke-wanken a kan Saminu. Ta sa hannu ta fisgo shi sai ga Saminu a cikin kwando ana jan kansa kamar wani rago. "Ga wani ƙarin naman mun samu, yau kam sai dai mahaifiyarsa ta haifo wani ba shi ba. Kunzuzuuuu ka zo ga irin jinin wanda kake so." Uwani ta ƙarasa zancen ta kai wa Saminu duka da farantin da ke ɗayan hannunta. Saminu na jin haka ya fara kiciniyar ƙwacewa, da ƙyar ya samu ya cire kwandon daga kansa. Shukra da Salim dama tuni suka shige ɗaki, daɗin da Shukra ta ji da ta ɗauki wayarta ta shiga da ita. Saminu na shirin fita a guje Uwani ta yi sufa ta datse ƙofar, sai da ta rufe sannan ta zare key ta ɗaga kanta ta wurga shi cikin bakinta. Da sauru ta kawar da kai gefe ta fito da shi ta soke mukullin, shi kuma da yake Saminu bai lura ba tuni cikinsa ya kaɗa. Uwani ta wage baki tana tauna da haɗiya kamar mai cin abu sannan ta ce. "Kamar yadda muka taune wannan mukullin haka za mu haɗiye ku ɗaya bayan ɗaya." Uwani na gama maganar ta ga fitsari na bin wandon Saminu, ta ɗauko robar yajin da Salim ya sha ya rage ta miƙa wa Saminu cikin wata irin murya ta ce. "Riƙe ka shanye shi tass, domin idan mun zo cin namanka mu ci shi da yaji-yaji. Idan ka shanye zan ɗauko maka mai galan guda ka shanye domin man jikinka ya yi mana kaɗan." "Don Allah ku yi haƙuri, ni dai tsautsayi ne ya kawo ni gidan nan." Saminu ya furta cikin zubar hawaye. Uwani ta suri wani ludayi ta ranƙwala wa Saminu, tun ba ta yi magana ba Saminu ya ɗauki robar yajin ya fara zazzagawa a baki. Yana sha yana hawaye ga wani azabar zafin yaji na ratsa shi. Numfashinsa ne ya fara yin sama, don haka ya ɓarke da kuka. A guje Uwani ta nufi ƙofar ɗakin da Shukra da salim suka shiga ta fara dukanta iya ƙarfinta. Hakan ya sa Saminu ya samu sukunin tashi a guje ya faɗa cikin kitchen ya rufe. Jin irin bugun da Uwani take yi ya sa Shukra cikin kuka ta kira Mami, Mami na ɗauka Shukra ta fashe da kuka sannan ta ce. "Mami na shiga uku, wallahi Uwani kashe mu za ta yi don Allah ku kawo mini ɗauki." Mami na shirin magana da mamaki ta ji Salim ya ɓarke da kuka, garjejiyar muryarsa ta ciki mata kunne. "Ke Shukra me kike faɗa ne? Kukan waye nake ji haka?" Bam! Bam! Bam! Mami ta ji ƙara ta cikin waya. Salim ya yi sauri ya fisgi wayar a hannun Shukra cikin garjejiyar muryarsa yana kuka ya ce. "Mami don Allah ki kawo mana ɗauki, wallahi aljanun Uwani hallaka mu za su yi." Jin da gaske Uwani na shirin karye ƙofar ya sa Shukra ta sake fashewa da kuka . "Ku saurare ni da kyau ku ji, wallahi ni nan da kuka gan ni na fi ku shiga tashin hankali. Uwani dai ga dukkan alamu tana da alaƙa da aljanu..." Mami ta kwashe duk abin da ya faru da tsakaninta da bunsuru, sannan ta ɗora da cewar. "Don haka ni yanzu babu wani taimako da zan iya yi muku, ni dai wallahi har abada na bar muku Uwani ta zauna a wurinku. " Daga haka Mami ta kashe wayar. A daidai lokacin Uwani ta samu nasarar karye ƙofar ɗakin, ƙofar na faɗuwa sai ita ma ta faɗi a ƙasa yaraf. Daga Shukra har Salim aka rasa mai motsi saboda tashin hankali. Suna son fita daga ɗakin suna jin tsoro saboda Uwani da ta yi kwance a bakin ƙofar,sai bayan wani lokaci ta ɗan fara motsawa a hankali. Tashi zaune Uwani ta yi tana jera atishawa tana murtsuka idanu, ta fara kallon su Salim da yanayin mamaki sannan ta miƙe tsaye ta ce. "Aunty Shukra lafiya na ga kina kuka ko jikin ne?" Gaban Shukra ya faɗi, amma sai ta ƙaƙalo murmushin yaƙe ta ce. "Cikina ne yake ciwo wallahi." Uwani na kai kallonta wurin ƙofar da ta karya ta dafe ƙirji a tsorace ta ce. "Na shiga uku, wannan ƙofar fa." Salim ya ƙarasa yana goge ƙwalla cike da yaƙe ya ce. "Ɗazu me gyara ya zo duba ta dama can matsala take ba mu, ai mai gyaran yana gidan ma bai tafi ba." Uwani a zuciyarta ta ce. "Ƙananan 'yan iska ni za ku mayar shegiya da." Fita ta yi daga ɗakin kai tsaye ta wuce kitchen ta buɗe ƙofar, Uwani na ganin Saminu ta ƙwalla ƙara tana faɗin. "Yaya Salim wani ya shigo mana gida, fito-fito wallahi ga shi nan a kitchen. Ko dai ɓarawo ne ma ka ga duk ya sauke mana labulen falo." Saminu da mamaki yake bin Uwani ya ga duk ta wani sauya kamar ba ita ba, yana fitowa ko ya shiga aika wa da Salim harara. Yana son tambayar key don ya buɗe ƙofa ya fita yana jin tsoro. Uwani ta fara tattara kayan falon tana 'yar mita. "Don Allah wa ya hargitsa ɗakin nan bayan jiya da dare tass na gyara shi." Shukra cikin tausasa murya ta ce. "Uwani bar wannan aikin ɗauko jakarki za mu wuce gida, ni ma da yake jikin na wa babu ƙwari gaban Mami zan koma." Uwani ba ta musa ba ta shiga ɗakinta, ta ɗan jima a ciki har su Shukra sun fara murna Uwani ta leƙo ta ce. "To ai Aunty Shukra na tuna Mami fa dama cewa ta yi na zauna sai kin warke. Haba don gyaran gidan ai ba wani wahala ba ne a wurina." Hawaye ya ciko idanun Shukra ta ce, "A'a gara dai mu je kin ga Salim tafiya zai yi ba daɗi ya bar mu, mu biyu a cikin gida." Uwani ta gyaɗa kai kamar mutuniyar kirki sannan ta shige cikin ɗakin. Tana shiga ta saka sakata, ta faɗa banɗaki ta yi wanka tana fitowa ta faɗa kan katifa ta kwanta. Babu jimawa bacci ya yi awon gaba da ita don har lokacin jikinta ciwo yake yi. Jiki a sanyaye su Daddy suka koma cikin gida don maganar da Lado ya yi abar dubawa ce, Lado yana tafe ban da zubar da ƙwallah babu abin da yake yi. Suna shiga cikin falon suka samu Mami tana kiciniya ita da ɗankwalinta, saboda tun fitar su Daddy take fama da shi da ta ɗaure sai ta ji kamar an fisge shi ya faɗo ƙasa. Ganin yanayin da Lado ya shiga ya sa jikin Mami ya yi sanyi, a dole ta shige ɗaki gabanta na faɗuwa fargabarta kada Lado ya tona asirinsu mutumcinta ya sake zubewa a idon su Dada. Aunty na ganinsu ta saki murmushi ta ce. "Hajiya Dada an fasa tafiya? Ai da ma daga zuwanki Dada ko ruwa ba ki sha ba ki ce za ki tafi." Dada ta jinjina kai cike da damuwa ta ce. "Ina zan tafi Lado da Saratu sun jangwalo mana jagwalgwalon masifa, kai ni kam tun da nake rayuwa na taɓa ganin jafa'i irin wannan?" Aunty ta yi sororo tana mamakin kalaman Dada. Daddy da kansa ya shiga ɗaki wurin Mami ya ce mata ta fito za su yi magana, tun da Mami ta ji haka jikinta yake karkarwa. A haka ta yi ta maza ta sako hijabinta tana sunne kai ƙasa, don jikinta ya gama ba ta akwai abin da yake faruwa. Zamanta a ɗakin babu jimawa, Daddy ya dubi Lado ya ce ya maimaita abin da ya faɗa dangane da Mami. Lado ya karkace kai ya fara wassafo jawabi tiryan-tiryan tun daga lokacin da aka fara ganin gawarwakin kajin Uwani, har zuwa lokacin da wannan mummunar ƙaddarar ta faɗa kansu. Mami tsumu ta yi cikin sanyin jiki kamar an jiƙa kaza a ruwa, Daddy ya dubi Mami cikin ɓacin rai ya ce. "Saratu wai yaushe za ki fahimci ɗa da dukiya ba a yi masa mugunta ne? Me ya sa idan kina wani abin tamkar ƙanƙanuwar yarinya? Yanzu wa gari ya waya? A tunaninki idan yarinyar nan ta ji abin da kika aikata raini ba zai shiga tsakaninku ba? Ko kina tunanin idan kika raba ta da kiwon da take yi kin gutsiri wani sashe a cikin rayuwarka." Tun da Daddy ya fara magana uffan Mami ba ta ce ba sai ruwan hawaye da ke zuba daga idonta, tun da ta zo duniya wannan karon ne na farko da ta far jin nadama dangane da abin da take aikatawa Uwani, ana cikin haka Malam mai Baƙara ya kira Daddy ya ce masa yana ƙofar gida. Daddy ya miƙe kenan zai fita Lado ya hango 'ya'yan bunsurun sun sake ɓullowa ta kusurwar bango, tsalle-tsalle suka fara yi suna dire-dire sannan suka tunkaro shi suna kuka. Daga gefensa ya ji bunsurun nan ya shafo masa ƙirji ya ce. "Lado fa sai dai ka yi haƙuri yanzu ma sun sake dawowa za su sha." A zabure Lado ya miƙe yana dafe ƙirji yana faɗin, "Don Allah ku taimaka mini wallahi yanzu ma sun zo za su zuƙe ni, wayyo Allah jama'a 'ya'yan bunsuru za su danne ni." Ganin da gaske sun yo kansa ya sa Lado ya yi sufa ya fisgo ƙafar Daddy da ƙarfi, sai ga Daddy ya dawo ta baya daɓar ya faɗi a ƙasa. Lado ya ji 'ya'yan awakin sun sake turmushe shi suna ƙoƙarin kai bakinsu jikinsa, da sauri ya janyo hannun Dada yana karewa a ƙirjinsa. Dada cikin tashin hankali ta zuba kabbara tana kiciniyar tashi daga gefen Lado tana faɗin. "Hasbunallahu wani'imal wakeel! Jama'a ku taimake ni zai saka mini hannu a ƙirjin aljanu." Lado da yake ganin ƙarfi da yaji awakin na turmutsa kai cikin ƙirjinsa ya sake warto ɗayan hannun na Dada yana dannewa. Dada ta fashe da kuka hankali a tashe sake cewa. "Allahu la'ilaha'ilahuwal hayyul ƙayyum! Mammam ku taimaki tsufa da tsohuwa baiwar Allah, don Allah ku agaza mini kada Lado ya sa ni ma su mayar da hi mata-maza." Dada na kuka ta ci gaba da biya Ayatulkursiyyu, lokaci ɗaya Lado ya nemi awaki da bunsurun ya rasa. Yaraf Lado ya faɗi gefe yana sauke ajiyar zuciya, Daddy ya miƙe yana kaɗe riga cike da takaici ya fita shigo da Malam mai Baƙara. Malam mai baƙara na shiga ya shiga gaisawa su baba Mustafa, har ƙasa ya tsugunna ya gaida Dada sannan ya mayar da kallonsa wurin Lado da ke sunne kai ƙasa. Ƙurawa Lado ido ya yi yana mamakin surarsa duk da kallo ɗaya ya yo masa ya fahimci akwai shafar jinnu a jikinsa. Daddy ne ya kora wa Malam jawabi sannan ya fita ya ɗauro alwala ya sa aka hura garwashi, ƙullin magunguna ya fara fito da su dangin su habbatus sauda. Sai da ya turara a ɗakin sannan ya fara biya karatun Alƙur'ani, a hankali Lado ya fara wata irin karkarwa idanuwansa na niyyar kakkafewa. "Assalamu alaikum Malam mai Baƙara! Ni sunana Malam Harisu." Wata murya ta furta ta bakin Lado. Malam ya amsa sannan aka sake cewa. "Malam ka fita a wannan yaƙin don girman Allah, saboda alƙawari na ɗaukar wa Mai shanu zan kare zuri'arsa akan kiwace-kiwacen da za su gudanar. Idan har ka ga ban tsoma kaina a ciki ba to faɗan na su sai ya kasance na cikin gida ne, kamar irin abin da ya faru tsakanin Uwar garke da Isuhu." Malam mai Baƙara ya jinjina kai sannan ya ce, "A wane dalili ne kai kuwa ka ɗauki wannan alƙawarin?" "Saboda na kasance Amini a wurin kakan Uwani wato Mai shanu, mun taɓa haɗuwa a cikin wani baƙin daji da rana tsaka a lokacin yana kiwon shanunsa. Ya yi mini wani taimako da na ji daɗinsa wanda silar haka ne, na ɗaukar masa alƙawarin duk rintsi zan kare zuri'arsa ta fannin kiwace-kiwacansu. Ko a lokacin da aka taɓa kai musu farmaki ba na ƙasar ne ina can yankin ƙasar India, bayan na dawo kuma ɗaya bayan ɗaya sai da na ɗauki mataki a kansu ko shi ban taɓa sanarwa ba sai yau da dalilin faɗar ta kama." Malam mai Baƙara ya jinjina kai ya ce. "Amma kai musulmi ne?" Ta bakin Lado aka amsa. "Ni cikakken musulmi ne gaba da baya." "To amma tun da kai musulmi ne me ya sa za ka cutar da waɗannan bayin Allahn, musulmin ƙwarai ai ba a san shi sa haka ba. Kamata ya yi su da suka aikata ba daidai ba in ma su nemi yafiyar mai awakin ko kuma Ubangiji ya yi musu sakayya." Malam mai baƙara ya jima yana yi masa nasiha sannan Aljani Harisu ya furta. "Tabbas kalamanka sun yi tasiri a kaina, kuma na ji duk wa'azin da ka yi mini. In shaa Allah ba zan sake aikata haka ba, amma wallahi da ka bar ni da su wallahi da sai dai su ƙare rayuwarsu a haka." Malam mai Baƙara ya yi murmushi ya ce. "A'a Dattijio Harisu ba za fa a yi haka ba, idan ka bar Lado a haka wacce macen ce za ta aure shi. Ka ga ai an cuci samartaka." Duk da a lokacin mutanen ɗakin na cikin alhini sai da suka murmusa. Dada ta yi kasaƙe sannan ta ce. "Wai Malam Harisu dai da na sani a shekarun baya mai zuwa wurin Malam?" Malam Harisu ya ce. "Ni ne dai Fillo ashe ba ki manta ni ba." Dada ta zaro ido waje ta ce, "Yanzu saboda Allah dama Harisu duk nono da man shanun da ka dinga kawo mini abincin aljanu nake sha ban sani ba?" Malam Harisu ya yi dariya ya ce. "Fillo ai ba za ki iya cin abincinmu ba, nono da man shanu kuma sayensu nake idan zan kawo wa maigidanki ziyara na kawo masa." Dada ta yi jim tana nazari sannan ta ce. "Kuma Malam ya san kai ba mutum ba ne kafin ya rasu?" Malam Harisu ya ce. "Tabbas na sanar da shi, kuma har ziyara na taɓa kai shi cikin dangina. Kuma ni na ce masa kada ya sanar da ke asalin wane ne ni, domin a halitta da ɗan adam mata akwai ku da tsoro." Dada ta yi shiru tana nazartar irin zaman mutumcin da suka yi da Malam Harisu, wani sabon tsoro ya shige ta don haka ta ja baki ta yi shiru. Daddy ya sauke ajiyar zuciya zai yi magana suka ji sallamar Jafar, kafaɗarsa ɗauke da jaka. Da mamaki duka suka dube shi, Dada ta yi saurin faɗin. "Wa nake gani kamar Jafaru?" Jafar ya yi murmushin gefen baki. Daddy cikin mamaki ya ce. "Jafar lafiya zuwa babu waya?" Jafar sai da ya sauke jakarsa ya zauna sannan ya ce. "Wallahi wata muhimmiyar magana ce ta kawo ni Daddy." Littafin kuɗi ne 500 za ki turo ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne🫠 Uwani sai da ta ci bacci ta ƙoshi sannan ta tashi ta sake faɗa wa banɗaki ta watsa ruwa, ƙugi cikinta ya shiga yi saboda yunwa don haka ta saka wata doguwar rogar atamfarta ta ɗauko ƙaramin hijabinta ta ɗora ta fito falo. Jungum-jungum ta ga su Shukra sun yi gaba ɗaya suna zauna a falon, kowanne ka dube shi fuska ɗauke da damuwa. Washe baki Uwani ta yi ta ce, "Aunty Shukra wallahi ina shiga ɗaki daga kwanciya bacci ya ɗauke ni." Shukra a ranta ta furta. "Lallai yarinyar nan kin raina mana hankali." Amma a fili sai ta saki murmushin yaƙe ta ce, "Ai da Baby har zai taso ki na ce ya ƙyale ki jiya kin sha aiki dole ki huta..." A zabure Salim ya katse Shukra, "A gidan Uban wa zan tashe ta?" Dariya ta so ƙwacewa Uwani sai ta basar, ta mayar da kallonta wurin Saminu da goshinsa ya yi wani malolo ta ce. "Ya Salim dama wannan mutumin bai tafi ba?" "Ba aljanunki sun haɗiye mukullin ba." Saminu ya faɗa a ransa. Uwani ta ɗago mukullin kamar ta san abin da yake ransa ta ce. "Ni wannan ko key ɗin ƙofa ne? Ina cikin bacci kawai ma ji an damƙa mini shi a hannuna." Da sauri Saminu ya karɓi mukullin baki na rawa ya ce. "Yawwa bari na je dama fa yanzu nake shirin tafiya." Saminu na buɗe ƙofa Salim ya yi caraf zai bi shi da sauri Shukra ta riƙo rigarsa ta ce. "Ina za ka tafi ka bar ni." Salim ya ce. "Office zan tafi baby." Shukra ta janyo shi ba ya ta ce, "Salim dama kana zuwa office ba ka yi wanka ba." Uwani a zuciyarta ta ce. "Yanzu wuya ta sa ba za a kira shi da Babyn ba ne?" Salim ya fara kiciniyar ƙwacewa don tun da ya samu hanyar fita, babu yadda za a yi ya zauna a cikin bala'i. Shukra ta sake fusgo shi ganin Saminu zai tsere masa ya sa Salim ya riƙo rigarsa yana faɗin. "Abokina don Allah kada ka tafi ka bar ni." Saminu ya juya ya doke hannun Salim, ya shiga kiciniyar ƙwace kansa ya ce. "A'a Salim wannan lamarin na ku family issuee ne daga yau kada ka sake kira a kan matsalarka." Lokaci ɗaya Saminu ya shiga fisgewa Salim na riƙe da shi, shi kuma Shukra ta ƙwaƙume rigarsa. Uwani ta saka hannuwa biyu ta toshe kunnenta ta ƙwalla ƙara tana ce wa, "Kaaaaaaaaiiii" A zabure gaba ɗaya suka fita a guje cikin tashin hankali. Gali mai gadi na zaune yana jin redio ya ga Saminu ya fito a guje yana faɗin. "Wayyo Allah jama'a ku taimaka aljanu za su ƙarasa illata ni." Jin takun Shukra a bayan Salim ya ƙara faɗar masa da gaba a zabure shi ma Salim ya zuba ihu yana faɗin, "Gali! Wayyo Gali ka kawo mini ɗauki, wallahi aljanu ne suka sauke danginsu a ciki." Gali miƙewa ya yi tsaye ganin mutanen gidan gabaɗaya sun fito suna ihu ya sa ya banka ƙofar ɗakinsa a guje ya danna saka. Nan take suka shiga 'yar tsere, Uwani ta dinga bin su tana kiran sunansu. Duk wanda ya ji an ambaci sunansa sai ya sake manna a guje, ita kuma Uwani ba ta yi ihu don ta tsora ta su ba, ta yi ihu ne domin ta ce musu dambarwar da suke yi ta yi yawa ba girmansu ba ne. Su kuma a nasu ganin sun yi tsammanin ko mutanen jikin Uwani ne suka sake dawowa suke kiran sunayensu. Uwani kan motar Saminu ta hau ta zauna don yunwa ta fara cin ta, ganin haka ya sa Saminu ya fakaice ta ya zare sakatar gidan ya fita a guje. Salim da Shukra na ganin haka suma suka fice Shukra daga ita sai hijabin sallah har ƙasa, ta ciki kuwa wata 'yar figigiyar rigar bacci ce a jikinta. Uwani na zaune ta hango Gali na hangenta ta windo, ta zaro masa idanu tana wani ƙambare hannu. Da sauri ya sauke labule cikin tashin hankali. Miƙewa Uwani ta yi ta koma cikin gida, ta buɗe firji ta ɗauko kaza duk ta yi ƙanƙara. Kayan miya ta ɗan jajjaga, ta tsoma kasar a cikin ruwa bayan ƙanƙarar ta narke ta yayyyanka ta ɗora farfesu. Ƙwai ta hango a kutchen ta ɗebo guda goma tana sakin murmushi, gabaɗaya ta fashe ta soya shi. Ta ɗora ruwan tea ɗan kaɗan daidai cikinta. Kafin wani lokaci Uwani ta haɗa kwanuka sun kusa biyar a gabanta, sai da ta je ta saka wa ƙofar sakata sannan ta bararraje tana faɗin. "Shegiya aunty Shukra dama tana da wannan kayan daɗin jiya ta bar ni da shinkafa, wannan gadon mugun hali da kika yi a wurin Mami dai ba ki gaji abin arziƙi ba. " Uwani ta yi maganar tana zuge cinyar kaza a bakinta, lumshe ido ta yi jin daɗi ya ratsa ta ta ce. "Yoo ai dama abinka da cikin mutumin ƙauye, dole na tuna Kura na ɗebi banza son raina. Tun da dama an ce waman taraka bati siddan, wanda ya ga ba ti ya ƙyale wahuwa jahilun shi jahili ne." Uwani tana cin abinci tana surutu sai ga shi kaɗan ta rage, ta ja gefe tana gyasa. Ɗaga can ta hangi A/C, hannu ta sa ta latsa ta ce. "A dole mu murji banza tun da babu a house. Allah Ya dai ya hore wa Daddy muma ya saka mana A/C ko ma ƙara jin daɗin duniya." Uwani na cikin surutu bacci ya yi awon gaba da ita. Fuska ɗauke da damuwa Daddy ya dubi Jafar ya ce. "Wacce irin muhimmiyar magana gare ka?" Jafar ya ce. "Jiya da daddare aka saki list na P-SKEEPING to sunana yana ciki za a yi refferel ɗinmu zuwa ƙasar Sudan, abin da ya kawo ni zan je Bompai akwai form ɗin da zan cike na yi submitting a can. Jirgi muka biyo ni DC Musa Jobe, shi ya sa ma ban kira ba." Shiru Daddy ya yi sannan ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Shi kenan Allah Ya bada sa'a ya tsare ku a duk inda kuke." Jafar ya lura da sanyin jikin mahaifinsa don haka ya saki murmushi ya ce. "Ai ba daɗewa za mu yi ba Daddy, ina jin bai fi shekara ɗaya zuwa ɗaya da rabi ba." Daddy zai yi magana Dada ta katse shi da cewar. "Wai Jafaru za a kai Sudan aiki? Magana ta gaskiya babu inda za shi, kai Mamman ba ka jin labarin kashe-kashen da ake yi. Maza kira mini shugaban 'yan sandan na duk duniya wallahi sai na sa ya sallami Jafaru daga aiki." Gudun kada Dada ta ja maganar ya sa Baba Mustafa ya ce. "Yanzu dai bari mu gama da wannan matsalar sai a ji da ta Jafar ko Dada?" Dada ta kalli Mami da ke sunkuye ta ce, "Duniya da Lahira dai Jafaru ba zai ga matsala ba, Saratu da Lado dai sune a cikin matsala dumu-dumu." Malam ne ya yi gyaran murya sai ya tambayi Malam Harisu a yaushe ne zai mayar da su Lado yadda suke, Malam Harisu ya ce. "Shi kam Lado a daren yau ma zai koma yadda yake, wato cikakken namiji. Ita kuwa Saratu sai dai ta yi zaman jiran tsattsafowar gashi. Don ina kwashe mata gashin kanta Zuwaira jikata ta ƙone shi. Saboda haka sai ta jira zai tsattsafo a hankali." Ya nuna Mami yana ci gaba da faɗin, " Kuma daga yau ki daina saka hassada, baƙinciki ko ƙyashi a kan abin da wani yake da shi. Idan ba haka ba kuma watarana sai kin kai kanki wurin da za ki kashe kanki, domin kowa kika gani a duniya da arziƙin da Allah Ya ƙaddari zai samu. Wani ba ya taɓa yi wa wani arziƙi don haka ki cire wannan baƙin ƙadarin na zuciyarki, abu na gaba da zan faɗa miki kuma ki samu mai kiwon ki nemi yafiyarta idan ba haka ba ki tafi da haƙƙinta." Shiru wurin ya ɗauka, kan Jafar ya ɗaure yana mamakin kalaman Lado, sai dai ganin sauyin hallitar Lado ba ƙaramin mamaki ya ba shi ba. A ɓangare ɗaya ya sake mamakin dalilin da zai sa Lado ya faɗa wa mahaifiyarsa maganganu mafara daɗi haka. Mami shiru ta yi tana gyaɗa kai, sai dai har a ranta ba ta jin za ta iya samun Uwani ta nemi yafiyar ta, don tsanarta tana nan a zuciyarta ba ta sauya ba. Malam mai Baƙara ne ya yi wa Malam Harisu godiya sannan suka yi sallama, Malam Harisu ya dubi Dada ya ce. "Fillo to sai yaushe zan sake kawo miki ziyara?" Dada ta waro ido waje ta ce. "A'a Malam Harisu zumunci kam wanda ya haɗa mu ai ya raba ko? Ni dai sai dai in ce Allah ya bada ladan wanda aka yi a baya." Mutanen wurin suka saka murmushi don kowa ya ji yadda Dada ke magana ya san a tsorace take. Ba a ɗauki lokaci ba Malam Harisu ya yi musu sallama, lokaci ɗaya Lado ya faɗi yana wata irin atishawa. "Daddy wai me yake faruwa ne?" Jafar ya tambaya. "Ga mahaifiyarka nan ita ya kamata ka tambaya, tun da har yanzu ta gagara gane Annabi ya faku." Daddy ya faɗa cikin zafin rai. Dada ta taɓo Jafar ta ce. "Yoo Jafaru yau dai na ga ƙarshen Saratu, ashe Saratu ce take sa ake kashewa Uwani dabbobinta." Nan take Dada ta zayyane wa Jafar abin da ya faru, ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba. Ya furzar da iska mai zafi a hankali ya ce. "Allah Ya kyauta." Dady har bakin gate ya raka Malam mai Baƙara sannan ya ɗauko sadaka mai kauri ya ba shi, yana shirin rufe ƙofa ya ga Adaidaita sahu ya sauke su Shukra ita da Salim. Kallon su ya yi duk a hargitse ko takalma babu a ƙafarsu, Shukra na ganin Daddy ta faɗa jikinsa ta fashe da kuka. "Salim lafiya me ya faru? Ina Uwanin wani abu ne ya same ta?" Daddy ya tambaya a rikice. "Alhaji ku ba ni kuɗina zan wuce." Mai Adaidaita sahun ya faɗa. Daddy ne ya zaro kuɗi ya miƙa masa, ya riƙe hannun Shukra suka shiga ciki Salim na biye da su fuskarsa duk ta yi zumu-zumu. Suna shiga ɗakin gaba ɗaya aka bi su da kallo, sai a lokacin Daddy ya ce wa Lado ya fita ya zauna a waje. Har suka zauna kuka Shukra take, Baba Mustafa ya dubi Salim ya ce. "Kai Salim lafiya me yake faruwa muka gan ku haka." Salim ya shafo gefen bakinsa da ya kumbure suntum ya ce. "Aljanun wannan yarinyar Uwani ne suka yi mana duka." Da sauri Jafar ya ɗago kafin kowa ya yi magana ya ce. "Uwani kuma? Me ya kai Uwani gidanka?" Jafar ya faɗa rai a ɓace. Daddy ne ya faɗa masa abin da Mami ta gaya masa dangane da rashin lafiyar Shukra da kuma tafiyar Uwani. "Dama Uwani na da aljanu? An ya kuwa Shukra haka kawai Uwani za ta tayar da iska? Na tabbata ruwa ba ya tsami banza, dole akwai dalili." Daddy ya yi maganar yana kafe su Salim da kallo. "Salim ne ya mare ta." Shukra ta faɗa, da sauri shi ma Salim ya ce. "Muka dai mare ta kema ba mari biyu kika yi mata ba?" "To ƙarfina da naka ɗaya ne? Ai marinka ya fi nawa, kuma kai ma mari biyun ai ka yi mata..." A zafafe Jafar ya katse Shukra da faɗin. "Ya isa! Don tsabar rashin mutumci matar tawa ce wani ƙato zai sa hannu ya mara? Kana da hankali kuwa Salim, wallahi sai na nuna maka kai ƙaramin ɗan iska ne gobe ba za ka sake aikata makamancin haka ba. Kuma daga yau ban lamunce Uwani ta sake zuwa gidan kowa ba tare da an sanar da ni ba." Saboda tsabar ɓacin rai Jafar ya manta da su Daddy da ke gabansa, daga Baba Mustafa, Daddy, Dada da Aunty ba ƙaramin daɗi suka ji ba ganin yadda hakan ya ɓata ran Jafar. Ban da Mami da ta yi sororo tana mamakin wai yau Jafar ne a gabanta yake iƙirarin Uwani matarsa ce, har a kan an mare yake tayar da jijiyoyin wuya. Baba Mustafa ya dafa Jafar ganin jikinsa na rawa ya ce, "Zauna Jafar." A daƙile ya zauna yana huci zuciyarsa na ɗaci. "Yanzu ina Uwanin take?" Daddy ya tambaya. Cikin haɗin baki a sanyaye suka ce. "Mun baro ta a gida." Don yadda Jafar ya birkice musu ba ƙaramin tsorata suka yi ba. Jafar na jin amsar da suka bayar ya miƙe yana faɗin, Daddy ina key ɗin motarka zan je na ɗauko ta." Daddy ya ɗauko key ya miƙa masa don shi kansa ransa a ɓace yake, ya tabbata kuma duk wannan abin da ya samu sake ne daga wurin Mami tun farko. Uwani sai bayan wani lokaci ta farka, ta kwashe kwanikan da ta kai su kitchen. Brush ta sake yi sannan ta fara haɗa kayanta tana murmushi, don ta san duk inda su Shukra suke yanzu sun kai wa su Daddy rahoton abin da ya faru. Wayarta ta ɗauko ta ga misscall rututu, gaba ɗaya na Jafar ya fi yawa. Haka kawai ta ji gabanta ya faɗi, tana shirin kiransa ta ji bugun gida kamar za a ɓalle ƙofar. Ta window ta leƙa bayan Gali ya buɗe masa ta hango shi ya shiga cikin gidan. Zaro ido ta yi tana mamaki, da sauri ta buɗe ƙofa ta fita a lokacin har ya fara ƙwala mata kira. Turus ta yi a gabansa tana mamakin yaushe ya zo garin, ya ƙarasa gabanta a hankali ta ce. "Ya Jafar kaine da gaske, don Allah yaushe ka zo garin?" Ƙura mata ido ya yi ya ga fuskarta ta ɗan kumbura, ga kumburun mari ga kuma na baccin da ta yi. Bai amsa mata ba ya saka hannunsa ya shafa gefen fuskarta. "Wuce mu tafi." Ya furta mata a taƙaice. "Bari na ɗauko jaka ta." Uwani ta yi maganar tana juyawa, a gaggauce ta ɗauko jakarta da duk wani tarkacenta ta fito. Gali ya bi ta da ido yana mamakin yadda ta sauya lokaci ɗaya kamar ba ita ce ta biyo masu gidan da gudu ba. Uwani na shiga mota Jafar ya dube ta ya ce, "Uban waye ya ba ki umarnin zuwa gidan Shukra?" "Mami ce." Uwani ta yi maganar tana ɗauke kai gefe. "Ba Mami ba daga yau ko Daddy ne ya ce ki tafi wani wurin ba ki sanar da ni ba wallahi sai na ɓata miki rai. Mami ce take aurenki ko ni?" Uwani ta taɓe baki ta ce. "Ni fa kada ka sauke mini kwandon faɗa a kaina, atoh. Ba babarka ba ce, tun da ita ta haife ka kuma ita ta ce na zo gidan 'yarta sai na wani bi ta kanka. Wai ni Ya Jafar ma me ya kawo ka lokaci ɗaya?" Jafar bai amsa mata ba ya ci gaba da kallon titi. Uwani ta sake taɓe baki ta ce. "Wallahi duk wannan shan ƙamshin da kake yi mini matsayinmu ya kusa zuwa ɗaya, ai saura bai fi shekara ɗaya da rabi mu yi candy ba. Idan na zama 'yar sanda sai mu dinga hura wa juna hanci." Uwani haka ta yi ta zuba ba tare da Jafar ya tanka mata ba har suka zo gida. Faɗa sosai Daddy ya yi wa su Shukra, sannan ya sake jaddada maganar Jafar a kan koda wasa kada a sake tura Uwani wani wurin ba tare da izinin mijinta ba. Ya kuma ba wa Uwani haƙuri a kan abin da ya faru, shi kansa Jafar sai da Daddy ya haƙurƙurtar da shi sannan ya haƙura. Daga haka kuma ya ce su tashi su tafi, ko Auta ba za ta je ta yi mata aiki ba. Idan har mai taya ta aikin suke buƙata sai dai Salim ya ɗauko mata mai aiki. Shukra tana kuka haka ta saka ƙafa ta fita ita da Salim, da za su tafi gida ma sai Daddy ne ya ba su kuɗin mota. Lado ya ba wa Salim takalminsa ita kuma ta saka na Mami. Miƙewa Jafar ya yi zai wuce sashensu, Aunty ta yi wa Uwani wani kallo da sauri ta tashi tana murmushi ƙasa-ƙasa don ta fahimci abin da take nufi. Da sauri ta je kusa da Jafar, ta saƙalo shi da hannu tana faɗin. "Wai Ya Jafar wacce tsarabar ka kawo mini? Ni fa ka san ciki na sa a gaba." Su Daddy murmushi suka yi, Dada cikin jin daɗi ta ce. "Oh Allah ka nuna mini ranar da zan ga 'ya'yan Jafaru da Uwani." Cikin sauri Aunty ta amsa da Amin. Wani malolon baƙin ciki ya turniƙe zuciyar Mami, tana raya sabon matakin da za ta ɗauka na wargaza tsakanin su, don ba ta fatan ta ga ranar da Uwani za ta haife jinin Jafar. Kamar wani sa'anta haka Uwani take tafe tana sake saƙale shi sai kuma ta buga tsalle idan ta yi magana ɗaya biyu. Bai tanka mata ba har sai da suka shiga ya zauna a gajiya, a gefen kujerarsa ta zauna ta yi shiru ta ce. " Wai sai magana nake Ya Jafar ka yi banza da ni." Kan kujerar da ya ke kai ya dawo da ita sannan ya shiga shafa fuskarta ya ce. "Ai ke ce ba ki iya tarba ba, dama haka sauran mutane suke yi wa mazajensu? Ko haka kika ga Aunty tana yi wa Daddy?" Da sauri Uwani ta rufe baki tana dariya ta ce, "Kambalastin ka ga yadda Aunty take ji da Daddy, yasin ko kunyarmu ba ta ji wani lokacin." Jafar ya saki murmushi ya ce. "To kin gani, ke kuma da kin gan ni sai dai ki tambayi tsaraba. Wai ma Uwani kina abin arziƙi a makaranta?" Uwani ta ɗan ɗaure fuska don ba ta san raini ta ce. "To Ya Jafar ka ɗauka asarar kuɗin tara Daddy yake yi? Bari ka ji in faɗa maka, to yanzu ni ce assistance monitor a class ɗinmu." Ya ji daɗi sosai a ransa sai ya basar ya ce. "Ke za a ba wa assistance monitor waye shaida?" Uwani ta tashi ta riƙe ƙugu sannan ta ce. "Ka tambayi Daddy mana, ai shi yake karɓo result ɗinmu." Jinjina kai ya yi sannan ya ce. "To zauna muyi magana." Jin yadda Jafar ya yi magana ya sa gaban Uwani ya faɗi don har ga Allah ta yi tsammanin maganar aurensa da Safna zai yi mata. "Wannan zuwan da na yi na zo yin wasu cike-cike ne, sannan kuma na zo mu yi sallama da ku. Sakamakon In shaa Allah next week za mu wuce ƙasar Sudan, kasancewar sunana yana cikin jerin ma'aikatan da za a aika daga nan ƙasa Najeriya zuwa ƙasar Sudan. Domin kwantar da tarzomar da ke tashi a cikin ƙasar." Jin haka ya sa Uwani ta zaro ido waje, Jafar ya yi murmushi ya ci gaba da cewa. "Kin san aikinmu dama ya gaji yawo, don haka ina fatan za ki taya ni da addu'a. Saboda yanayin hatsarin wurin da za mu fuskanta, kuma dama tafiya ƙarin ilimi ce sannan duk abin da ya faru da bawa rubuce yake a cikin kundun ƙaddararsa." Jafar na zuwa nan a zancensa sai gani ya yi Uwani ta rushe da matsanancin kuka. Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Kukanta yake ji har cikin ransa, ya janyo ta jikinsa a hankali ta sauke ajiyar zuciya yana buga bayanta cikin wata irin murya ya furta. "Kukan kuma na mene ne?" Hawaye bibbiyu suka ci gaba da shatata daga idanun Uwani, ya saka hannu ya goge mata yana mamakin kukanta. "Gaskiya ni dai kada ka tafi Ya Jafar wallahi tsoro nake ji." Murmushi Jafar ya saki ya ce. "Tsoron me Uwani?" Shiru ta yi ta kasa magana saboda yadda ƙirjinta ke bugawa. "Ko tsoro kike ji kada a kashe ni? Ba ke kika ce idan muka rabu za ki auri mai ƙaunarki ba? Ko kin manta?" Idanun Uwani suka sake zubo da ƙwalla, ta kwantar da kanta a ƙirjinsa har cikin jikinsa yana jin bugun zuciyarta. "Ai wannan ba mutuwa ba ce, kawai dai idan ka sake ni ne zan auri wani tun da kai ma Safna kake so. Amma wallahi ba na son ka tafi, ba na son wani abu ya same ka." Har a ransa ya ji zafin kalaman Uwani, wato har yanzu dai ba ta jin irin abin da yake ji a kanta. "To wanda ba ka son shi don ya mutu damuwar me za ka yi? Kin ga dai tun da ba kya sona ko na mutu shi kenan Safna ce za ta ji babu daɗi." Shiru Uwani ta yi tana jin zuciyarta na zafi, tsam ta tashi daga kusa da shi fuska babu walwala ta ce. "Tun da haka ka gani shi kenan, dama ka sha faɗa mini Safna ita ce zaɓinka. Ni dama ka ga auren haɗi aka yi mana, tun da haka ne don Allah ka sake ni kafin ka yi tafiyarka. Ka ga shi kenan babu takaba a kaina, idan ya so sai a ɗaura maka aure da Safna kafin ka tafi. Duk tsiya dai na san babu abin da figaggiyar budurwarka za ta nuna mini." Uwani na gama magana ta shige uwar ɗaki, kan gado ta faɗa ta saki wani marayan kuka. Tun daga farkon kalaman Uwani tsaf Jafar ya fahimce cike suke da zallar kishi, maganarta ta ƙarshe ta ba shi dariya wai figaggiyar budurwarsa. Miƙe wa ya yi ya shiga ɗakin har zai mata magana ya lallashe ta, sai ɗayar zuciyarsa ta gargaɗe shi da faɗin. "Ya kamata ka rage rawar kai a kan yarinyar nan, kar ka zo raini ya shiga tsakaninku." Toilet ya faɗa ya yi wanka har ya fito Uwani na kwance, bayan ya shirya ne ya nufi sashen Mami. Bayan fitar su Jafar 'yar hira su Dada suka taɓa, baba Mustafa ya ce zai tafi ita ma Dada ta ce su wuce tare. Sai da su Dada suka sauka sannan Mami ta iya motsawa ta koma ɗakinta, Aunty har bakin gate ta raka su sannan ta koma ta shiga kitchen don ranar ita ce da girki. Lado yana nan zaune yana bin su da kallo jiki a sanyaye, sai da Daddy ya raka su har zai koma Lado ya sha gabansa ya sake ba shi haƙuri a kan abin da suka aikata. Daddy ya yi masa nasiha sosai sannan ya ce masa ya samu Uwani ya nemi yafiyarta, ko ba komai zai sauke nauyi daga kansa. Jafar na shiga sashen Mami a zaune ya same ta a kan kujera, bayan ya sake gaishe ta ya yi mata kallon tsaf ya ga duk ta rame ta lalace. Yana shirin fara magana Mami ta furta. "Wato kai yanzu Jafar ina yi maka kallon mai hankali ashe kai shashasha ne ba ka da tunani? Duk huɗubar da nake yi maka a kan yarinyar nan ya tashi a iska? Jafar yanzu a kan Uwani ne har ya kake tayar da jijiyar wuya a kan idona, saboda ƙanwarka da mijinta sun mare ta." Ɗago wa ya yi zuciyar sa na zafi ya kalli Mami, ya sassauta murya ya furta. "Mami ko ina son Uwani ko ba na son Uwani matata ce kuma a ƙarƙashin ikona take, duk fa wani haƙƙinta yana kaina. Yanzu kina ganin ko mijin Shukra zai zauna wani ƙato ya mari matarsa ba tare da ya ɗauki mataki a kai ba? Mami don Allah ki fahimci ni, amma abin da kike yi fa ya yi yawa. Ki duba ki ga fa saboda Uwani kin kusa jefa rayuwarki a cikin wani halin ina amfanin haka? Yanzu kina ganin Dada ba za ta sanar da sauran 'ya'yanta abin da ya faru ba? Mami ba kya tunanin irin kallon da mutanen Kura da duk wanda ya ji labarin nan zai yi miki?" Jafar ya haɗa hannuwa biyu alamar roƙo sannan ya ci gaba da cewa. "Na haɗa ki da girman Allah Mami ki fita a harkar Uwani, aure ne dai na faɗa miki zan auri Safna ƙarshen magana ma ga shi har iyaye sun shiga ciki. Na sha faɗa miki Safna ita ce zaɓina ita nake so to me zai dame ki? Wallahi Mami ina tsoron lokacin da Uwani za ta dinga mayar miki da martani domin yau da gobe ta fi ƙarfin wasa." Tun da Jafar ya fara magana Mami take wurga masa harara sai da ta ji ya gama magana sannan ta ce. "Wallahi har abada ba na jin zan ƙaunaci tsinanniyar yarinyar nan a cikin zuciyata, duk wannan sharhin da kake yi na fuskanci inda ka dosa amma da sannu kai ma zan gyara maka zama. Idan ka gama tashi ka fita ka ba ni wuri." Mami ta ƙarasa maganar tana nuna masa ƙofa. Ganin Mami ta ɗauka da zafi ya sa Jafar ya saki murmushi ya ce. "Tuba nake ranki shi daɗe, yanzu dai Mami mu bar wannan zancen. Cikin wata na gaba nake son fara haɗa lefe, amma kafin nan akwai kuɗaɗen da za a biya mu kafin mu tafi ina son Daddy zai saya mini fuloti a unguwar Mai dile." Jin daɗin maganar Jafar ta haɗa lefen Safna ya wanke laifinsa a ranta, cikin farin ciki Mami ta ce. "To ko kai fa? Allah Ya nuna mana da rai da lafiya. Dama duk wani abin da ka sani irin na 'ya'yan manya za a yi, don kasan dai wane ne mahaifin Safna. Kuma idan ka tashi babban gida za ka gina mata don na fi son harkar girma, Allah dai ya kai ka wannan ƙasar lafiya ya dawo da kai lafiya." Jafar ya yi murmushi sannan ya amsa da Amin. Ya jima a wurin mahaifiyarsa suna hira, sannan ya fice daga ɓangarenta. Yana fita harabar gidan ya ga su Auta sun dawo daga makaranta, da gudu suka ƙarasa wurinsa suna mamakin ganinsa. Sai da suka ɗan taɓa hira sannan suka wuce ciki shi ma ya koma sashensu. Ko da ya koma Uwani zaune take tana game a wayarta, ko ƙurarsa ba ta kalla ba Jafar ya saki murmushi don ya fahimci fushi take da shi. Washegari tun da Uwani ta tashi sallar asuba ba ta koma ba, sai da ta haɗa musu breakfast a lokacin Jafar yana kwance. Sai da ta shirya komai ta ajiye shi a mahallinsa, sannan ta faɗa toilet ta yi wanka. A gurguje Uwani ta ci abinci saboda ta kusa makara, ta ɗauki jakar goyonta ta saka har za ta fita ta ji Jafar na faɗin. "Tafiya kuma babu sallama Uwani?" Tura baki gaba ta yi sannan ta ce, "To ba bacci kake yi ba! Ni dai na tafi Ya Jafar kar mu makara ." Tana gama maganar ta ji bugun ƙofa da sauri ta ƙarasa ta buɗe ƙofar, Auta ta gani a tsaye. Sai da Auta ta ɗan leƙa ta gefen Uwani ta yi ƙasa da murya ta ce. "Ni fa na ɗauka ma yau ba za ki ba, tun da na ji shirun ya yi yawa na ce ƙila kina can kina tsinkar fure." Uwani ta ɗaka wa Auta duka a baya ta ce. "Wallahi Auta ki fita idona, kin raina ni da yawa me kike nufi." Auta ta ƙunshe baki ta ce. "Abin da kike nufi mana, wai ma me ye sirrin ne yasin na ga yau har wani fresh kika yi. Ni fa ina tsoron wallahi kada mu je ana wa'ec kina fama da tumbi a gaba." Auta ta ƙarasa maganar ta yin gaba don ta san tsaf Uwani za ta sake kai mata duka, Uwani ta riƙe baki tana murmushi ta furta. "An gaya miki mu haka muke? Ni fa Auta wallahi kin fi ƙarfi bari mu dawo da kaina zan samu Daddy, na gaya masa gaskiya gara Dr kawai ya turo." Da sauri Auta ta marairaice don ta san ba ƙaramin aikin Uwani ba ne ta aiwatar da abin da ta faɗa, ta ƙarasa ta saƙalo Uwani cikin kwantar da murya ta ce. "Haba matar yaya kada mu yi haka da ke." Uwani ta bushe da dariya ta ce. "Ashe dai iskancin na ki na ƙarya ne." Gaba ɗaya suka saka dariya. Suna nan tsaye Ibrahim ya fito ya shiga mota, su Uwani suka buɗe suka shiga ya wuce da su makaranta. Kamar yadda Malam Harisu ya faɗa ko da Lado ya wayi gari da asuba sai ganinsa ya yi ƙirjinsa ya koma daidai, ya jima yana hamdala ga Ubangiji. Kuma da asubar bayan Daddy ya dawo daga sallar asuba Lado ke sanar da shi yadda ya wayi gari. Takardunsa masu muimmamci Jafar ya ɗauka bayan ya yi wanka ya ci abinci ya shirya, kai tsaye Bompai ya nufa domin cike duk waɗansu muhimman abubuwan da suka kamata. Sai yamma liƙis ya dawo a lokacin su Uwani suma sun dawo daga makaranta, Aunty ce ta sa Uwani ta girka wa Jafar tuwon semovita miyar kuɓewa ɗanya. Ya ji daɗin abincin don haka ya zage ya ci tuwon sosai, yana ci yana santi Uwani sai murmushi take bayan ya gama suka wuce sashen Daddy. Jafar ya wuce ɓangaren Mami Uwani kuma ta wuce ɓangaren Aunty, tana shiga ta samu Auta suna hira. Cikin zuga da shaida Auta ta ce. "Aunty kin ga Uwani a tsohon daren nan ko ina ta bar Ya Jafar?" Aunty ta yi murmushi don ta fahimci da biyu Auta ta faɗi haka. Uwani ta kai wa Auta ranƙwashi a ka ta ce. "To munafunfun ai tare muke, shi ma ya shiga sashen Mami." Daga haka suka ci gaba da hira, ita kuwa dama Madina 'yar ɗakin Mami ce, saboda tun da Aunty ta zo gidan ba ta shiga sashenta ya kai sau biyar ba. Kasancewar yau ta kasance asabar ya sa Jafar ya ce Uwani ta shirya za su fita, kuma a wannn ranar saura kwana ɗaya ya koma Lagos, tun da ta can za su wuce shi da abokan aikinsa. Uwani baki har kunne don a cikin ziyarar da su kai ya ce mata har da gidan mahaifiyarta, tare da Auta suka tafi duk da a farko Mami ta so hanawa amma Daddy ya ce su tafi tare. Can dangin Mami suka fara zuwa sun ɗan zazzaga gidanjen 'yan uwanta, kuma babu yabo babu fallasa suka tarbi Uwani. Daga nan Jafar ya wuce da Uwani can garin da mahaifiyarta take aure, lokacin da suka je Aramma ba ya nan. Amma yanayin yadda Uwani ta samu mahaifiyarta da kishiyarta Indo ba ƙaramin burge ta ya yi ba. Gidansu tsaf su da yaransu fes ba kamar da ba, da kowa ya gan su yana san suna cikin wahala. Haka a ɓangaren cima duk da Innarta ba ta san da zuwan su ba samu suka yi sun yi tuwon shinkafa miyar taushe har da nama a ciki, saɓanin a baya da ta ji Indo na ƙorafin kullin tuwon dawa suke ci sai dai Aramma a tuƙa masa tuwon shinkafa, ko idan ya je cikin gari ya taho da semovita a tuƙa masa. Marayama ta ji daɗin ziyarar da su Uwani suka kawo mata, saboda kara dama tun da aka yi auren Uwani sau uku ta taɓa zuwa wurinta. Sai dai zuwan farko da na biyu da ta yi sam ba ta ji daɗi ba ganin irin tarbar wulaƙancin da Mami ta yi mata, amma zuwan Aunty gidan ya sa wata rana da ta taɓa zuwa ta karɓe ta hannu bibbiyu. Sun sha hira sosai sai yamma liƙis sannan Jafar ya zo tafiya da su. Nasiha sosai Maryama ta yi wa Uwani don ta ji daɗin ganin yadda Uwani ta sake nutsuwa a kan da, Maryama godiya ta yi wa Jafar sosai lokacin da ta rako su. Ya ɗauko wata ƙatuwar leda a mota ya miƙa mata da kuɗi naira dubu goma, da farko Maryama cewa ta yi ba za ta karɓa ba sai da ƙyar ta karɓa Jafar na yi mata magiya. Za su shiga mota kenan Aramma ya ƙarasa ƙofar gidan yana washe baki ya ce, "Yau manyan baƙi ne a gidan namu?" Gabaɗaya suka russuna har ƙasa suka gaishe shi, Aramma ya zaro ɗari biyar-biyar ya miƙa wa Uwani da Auta. Jafar sai harara yake aika musu Uwani ta maze ta karɓa, ganin haka ya sa ita ma Auta ta karɓa. Lokacin da suka shiga mota faɗa Jafar ya shiga yi musu, a cikin su babu wacce ta tanka masa har suka ƙarasa. Gabaɗaya sashen 'yan uwan mahaifinsa sai da ya shiga ya yi musu sallama sannan ya koma ɓangaren Dada suka dasa hira. Ba su suka baro cikin Kura ba sai bayan sallar Magriba, lokacin da za su tafi Dada sai zubar da ƙwalla take tana jimamin tafiyar Jafar ƙasar Sudan. A daren ranar Jafar shi da Uwani suka haɗa kayan da zai tafi da su don gari na wayewa da sasssafe zai wuce, Jafar ya lura da sanyin jikin Uwani wani lokacin har ƙwalla take gogewa a fakaice. Washegari da sassafe Jafar ya shirya ya fito, su Mami duk suka fito rakiyarsa bakin gate. Mami ma zuciyarta duk babu daɗi, Daddy ne yake ƙarfafa mata gwiwa. Addu'a gabaɗaya suka yi masa, Uwani ta jingina da mota tana zubar da ƙwalla. Yana son ya yi sallama da Uwani don ya sake rarrashinta amma nauyin su Daddy ya hana shi, a fakaice yake kallonta fuskarta ta kumbura suntum sai goge ƙwalla take. Daddy ya dubi Jafar kamar ya san abin da yake ransa ya ce. "Ya kamata kafin ka tafi ka lallashi matarka, kasan har yanzu da ragowar yarinta a kanta." Daɗi Jafar ya ji, don haka ya kama hannun Uwani suka shiga cikin sashensu, suna shiga na su gate ɗin Uwani ta faɗa jikinsa tana fashewa da matsanancin kuka. Riƙe ta ya yi tsam kamar wani zai ƙwace masa ita. Bubbuga bayanta ya fara yi yana jin kukanta har cikin jikinsa, sai da ya ji ta ɗan tsagaita sannan ya ɗago da fuskarta ya furta. "Ɗigar hawayenki na zare mini ƙwarin gwiwar da je tattare da ni, kina son na tafi da rauni har na gagara gudanar da abin da zan je yi." Uwani ta girgiza kai tana hawaye. Jafar ya sa hannu ya lakace mata hawayen da ya gangaro sannan ya ce. "A yanzu addu'arki nake buƙata domin za ta yi tasiri a gare ni." Ya ɗauki hannun Uwani ya ɗora a saitin ƙirjinsa sannan ya ci gaba da cewa. "Da kin san tarin abubuwan da ke ƙunshe cikin zuciyata da kin jinjinawa gwarzo kuma jarumin mijinki, ki sa a ranki a kodayaushe ina tare da ke. Zan yi kewar bakin tsiwarki, zan yi kewar rigima da rashin jinki." Uwani ta saki murmushi tana jin wani shauƙi a ranta, cikin shagwaɓa ta ce. "Ni kuma zan yi kewar cin zali da muguntarka." Lokaci ɗaya suka saka dariya, Jafar ya janyo Uwani ya yi mata raɗa a kunne da faɗin. "Na jima ina dakon kalmar da muhallin da ya dace na furtata, zuciyata, ruhina da gangar jikina duka na sadaukar gare ki. Idan har ban bayyana miki mikin da ke cin zuciyata ba, ban san yadda zai ƙara girmama a cikin jikina ba. A duk hawa da saukar bugun numfashina, ina yin sa tare da so da ƙaunarki ne. Ina son ki! Ina ƙaunarki soyayyar da harshena ba zai iya fasalta irinta ba." Kusan mutuwar tsaye Uwani ta yi tana jin wani abu yarrr na zagaye ilahirin jikinta, tun daga tafin ƙafarta har tsakiyar kanta. Lokaci ɗaya wata irin kunyarsa ta kama ta, ta sunkuyar da kanta ƙasa tana murza yatsun hannunta tana murmushi. Ɗago kanta ya yi ba ta yi tsammani ba ta ji ya haɗe bakinsu wuri ɗaya, duk yadda ta kai ga jin nauyinsa sai ta samu kanta da mayar masa da martani cikin sanyin jiki. Ya ɗago cikin wani irin yanayi ya sumbaci goshinta jin Daddy ya fara yi masa horn, ya dubi Uwani cikin wani irin shauƙin so ya ce. "Ki kular mini da kanki, za mu yi waya idan na sauka." Jafar ya sake sakar mata kiss a goshi sannan ya riƙo hannunta suka fara takawa cikin sassarfa. Ilahirin mutanen da ke wurin bin Uwani da kallo suka yi ganin yadda ta fito tana murmushi, sallama ya sake yi wa su Mami ta amsa masa a gwasale don ba ƙaramin haushin Jafar take ji a kan kulawar da ta ga yana ba wa Uwani ba. A sanyaye Uwani ta bi motar Daddy da kallo har ta fice daga gidan, Auta ta zagaya ta bayan Uwani cikin zolaya ta ce. "A toh ƙaryar a yi mini iskanci ta ƙare tun da yanzu dai kusan ɗaya muke da mutum." Uwani ta wurga mata harara ta ce. "Gara da kika ce kusan ɗaya amma dai ba ɗayan muke ba ai." Auta ta ɗan haɗe fuska cikin sigar wasa ta ce. "Faɗa mini wai wane karatun Ya Jafar ya biya miki da kika fito kina murmushi, yasin kowa ya fahimci a yanayin da kuka fito ke da shi." Uwani ta saki murmushi tana jin tamkar a lokacin Jafar yake sake faɗa mata daɗaɗan kalamansa, ta dubi Auta tana ɗaga mata gira ta ce. "Malama daina ambatar mini sunan miji kada ki sa gabansa ya yi ta faɗuwa, yarinya ba kin yi nauyin baki ba na ce zan faɗa wa Daddy Dr ya turo kin hana. Ai ke ma da anfara biya miki irin karatun da ake biya mini." Auta ta yi cikin gida tana dariya haɗe da faɗin, "Wallahi Uwani kin fi ƙarfina sai ki goge mini hadda." Lokacin da su Jafar za su tashi sai da ya kira Uwani ya shaida mata sannan suka yi sallama, haka bayan da ya sauka ma bayan ya kira Mami da Daddy sai da ya kira ta. Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya su Uwani suna ci gaba da karatunsu, yayin da Jafar ke ƙasar Sudan yana gudanar da aiki. Yawancin hirar Uwani da Jafar ta whatsapp suke yi, wani lokacin har video call suke yi musamman idan ba shi da duty a wurin aiki. A wannan lokacin ne cikin Shukra ya tsufa, ganin haka ya sa Salim ya dawo da ita gida don gudun kada ba ya gida ciwo ya taso mata. Zaman Shukra a gida tsakaninta da Uwani babu yabo babu fallasa, saboda tun abin da ya faru take shakkar Uwani. Haka tsakaninta da Aunty sai gaisuwa amma ta daina yi mata kallon banza da habaici. A cikin wannan yanayin ne kuma ita ma Aunty ta fara wani irin zazzaɓi da ciwon ciki, ciwon Aunty ba ƙaramin tsorata Daddy ya yi ba. Hatta su Uwani sun tausaya mata ganin lokaci ɗaya ta yi wata irin rama, a ranar wata laraba ne ciwon ya matsanta mata ya sa Daddy ya ɗauke ta zuwa asibiti. Gwaje-gwaje aka yi mata, gaban Daddy sai faɗuwa yake musamman da ciwon cikin ne ya fi matsa mata. Yana fargabar kada a ce wani ciwon ne a cikin nata, da farinciki Dr Fadwa ta sanar da shi juna biyun da Aunty ke da shi, wani irin farin ciki ya mamaye Daddy ban da hamdala babu abin da yake yi. Da yake Mami ta je garin Kaduna wurin gaisuwar ƙanwar mahaifinta, ya sa ba ta san duk wainar da ake toyawa. Ganin farincikin da su Daddy ke ciki ya sa Auta da Uwani suka keɓe suna gulmar ko dai abin da suke zargi ne ya tabbata. A washegarin ranar ne kuma Shukra ta tashi da ɗan ciwon naƙuda sama-sama, don haka ta janyo jaka tana tafe da takalmi mai tsini ji kake ƙwas-ƙwas. Da Aunty suka haɗu Shukra na tafe tana cin cingam, da mamaki Aunty ta dube ta ta ce. "Shukra lafiya? Ina zuwa haka?" Shukra sai da ta yi wani ƙas ƙas da cingam sannan ta ce. "Labour na fara na kira Baby yanzu za mu wuce asibiti." Uwani da zuwanta wurin kenan ta dubi Shukra tun daga ƙasa har sama, a ranta ta ce. "Ko da ban san ciwon haihuwa ba amma Aunty Shukra da alama ba ki fara cin ƙwal ubanki ba." Cikin salon gulma Uwani ta yi hanzarin riƙo akwatin Shukra ta ce. "Sannu Aunty Shukra! Ina za ki iya sauka da wannan akwatin, bari mu je ni da Auta mu raka ki asibitin. Ita kuma Aunty ko ruwan zafi ta dafa mana." Shiru Shukra ta yi da kamar ba za ta amince ba sai kuma ta sakarwa Uwani jakar tana tafe tana hura cingam. Jin horn a ƙofar gidan ya sa Shukra ta yi gaba tana faɗin, "Uwani ke da Auta ku yi sauri ga baby ya ƙaraso, kada ku sa na haihu a mota." Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 Idan littafi ya kammala cmplt 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Har Shukra ta yi gaba Aunty ta bi ta tana faɗin, "Amma haihuwa Shukra kya tafi da su Uwani? Ba gara su zauna a gida ba ni mu tafi tare." Shukra sai da ta tauna cingam ta yi ƙwai da shi ta fasa sannan ta ɗan yamutsa fuska ta ce. "No gaskiya ba sai kin je ba, just haihuwa ce kawai fa sai mun yi wata gayya. Ki zauna a gida kawai kamar yadda Uwani ta faɗa." Shiru Aunty ta yi don ba haka ta so ba, amma jin abin da Shukran ta faɗa ya sa ta amsa mata. A daidai wannan lokacin ne Su Auta suka ƙarasa sanye da hijabansu, tirtsi-tirtsi haka Shukra ta ci gaba da tafiya da tsohon ciki tana cangala ƙafafuwa da takalmi mai tsini. Har su Uwani sun yi gaba Aunty ta gagara haƙuri ta bi su tana faɗin. "Uwani ki cire wayarki a silent zan kira na ji yanayin jikin nata an jima." Amsawa Uwani ta yi tana kallon irin yauƙin da Shukra take yi, suna zuwa bakin gate suka samu Salim ya yi parking ɗin motarsa. Sai da suka zauna sannan Salim ya lura da Uwani, a ɗan zabure ya kalle ta. Yana son ya yi magana yana jin tsoro, tafiya suka fara yi kai tsaye suka nufi Zoo road asibitin Siyam Clinic da yake a can Shukra take yin awo. Ta gaban Amnash Saloon za su gifta Shukra ta ɗan yamutsa fuska ta ce, "Baby ina son wanke kai kafin mu ƙarasa." Salim ya kalli ƙofar Saloon ɗin ya ce, "Amma baby ina tsoron kada ki haihu a ciki."Murmushi ta sakar masa a daidai lokacin ya yi parking ta ce. "In Shaa Allah har za a gama." Shukra ta waiga wurin su Uwani ta ce. "Ku fito za ku ɗan matsa mini ƙafa don na gaji." Uwani da Auta suka kalli juna ga gulma fal bakinsu ga babu damar yi. Shukra na fita suka bi bayanta, Hajiya Maryam mai saloon ɗin na ganinsu ta sakar wa Shukra murmushi saboda costomer ta ce. "Maman biyu na ɗauka kin sauka ma?" Hajiya Maryam ta furta. " Shukra ta sake ɗan gantsarewa ta ce. "Ga mu dai muna fama, yanzu haka ai labour nake." Jinjina kai Hajiya Maryam ta yi suka ƙarasa ciki, ba a ɗauki lokaci ba aka gara mata kai tass. Uwani da Auta suna tsugunne kamar 'yan aiki suna matsa mata ƙafafuwa, ana gama gyara wa Shukra gashi suka wuce asibiti. Ɗakin da aka kai Shukra su biyu da ita da wata matashiyar mata ita ma haihuwar fari za ta yi, amma ita har ta fara galabaita. A lokacin da Shukra ta shiga ne ta samu matar ta hau saman windon ɗakin, ta wala ƙafafuwanta tana faɗin. "Ya subahanallahi, Summassabila yassara. Dr Hussain don Allah ka zo wallahi jaririn zai koma mini wuya." A ɗan yatsine Shukra ta bi ta kallo ta ce, "Haba baiwar Allah mene ne haka kike yi? Yanzu idan Dr ya shigo ki ce masa me? Ko kunyar kanki ba kya ji sai wani yaye zani kike yi." Wani ƙululun baƙin ciki ya mamaye matar, ta sake maƙale window jin wani azabban ciwo ya murɗo mata ta ce, "Ya Allah ka ga wannan baiwar ta ka, Allah ka ɗauki cikina ka haɗa mata ta ji abin da nake ji." Shukra ta haye gado tana ɗaga waya tana selfie, tana sake gyara kwanciyar gashinta. Su Uwani suna reception suna zaman jiran haihuwar Shukra, ta kira Jafar ta whatsapp a nan take sanar da shi suna asibiti Shukra za ta haihu. Sun ɗan taɓa hira da shi sannan suka yi sallama, suka tambayi wuri za su yi sallah don lokacin har sallar azahar ta yi. Wani ɗan ɗaki aka nuna musu bayan sun yi alwala suka shiga, a nan ne suka samu wasu mata guda biyu, ɗayar ta idar ta fita sai wata yarinya suka gani da ba ta fi shekara goma sha shida zuwa sha bakwai ba. Uwani har za ta tayar da sallah ta ga jikin yarinyar ya ɓaci ta baya, da alama baƙon watanta ne ya zo ba ta sani ba. Da yake Uwani ta ga su uku ne kawai a ciki sai ta taɓo ta ta ce, "Kin ga sallarki ta karye fa na ga jikinki ta baya ya ɓaci." Yarinyar ta waiga a kunyace don ita ma ta san da halin da take ciki ta ce. "Tun da muka zo ne dama na ga ya zo mini, to sai dai har yanzu Auntyn da na rako ba ta haihu ba. Amma Hajiyanta ta kusa zuwa idan ta ƙaraso zan koma gida, bari dai na yi sallah kada Aunty ta buƙaci wani abin." Da mamaki Uwani ke bin yarinyar don ta fahimci tamkar ba ta san hukuncin abin da yake jikinta ba. Kafin Uwani ta yi mata magana har ta ƙara tayar da sallah, Uwani ta sake taɓo ta tana faɗin. "Kin san idan fa ana Period ba a yin sallah ko ba ki sani ba?" Yarinyar ta gyaɗa kai sannan ta ce. "Eh gaskiya ni ban sani ba don idan ya zo mini sallah kawai nake yi!" "Idan kuma ya tafi fa ya kike yi?" Uwani ta wurga mata tambaya. Yarinyar ta wara hannuwa ta ce, "Shi kenan ba wani abu da nake yi. Ni dama takura ni yake yi shi ya sa wallahi duk wata ba na son ya zo." Ajiyar zuciya Uwani da Auta suka sauke, Auta ta ce. "Ba kya zuwa islamiya ne ko ita Auntyn ta ki ba ta koya miki ba?" Take idanun yarinyar suka ciko da ƙwalla, a sanyaye ta ce. "Lokacin da nake garinmu Innata ta saka ni a makarantar dare, to sai mahaifina ya cire ni ya sa aka kawo ni aikatau. Yanzu shekara ta huɗu kenan a garin nan, dama tun ina yarinya na fahimci mahaifina ba ya ƙaunata. Ita ma Innata da tana sona amma tun da, Ladidi dillaliya ta ba ta labarin kuɗin da ake samu a gidan aikatau shi kenan ta daina sona, saboda da sa hannunta aka kawo ni birni wai na tara kuɗin kayan ɗakin aurena." Yarinyar ta ƙarasa maganar tana hawaye, sai da share ƙwalla sannan ta ci gaba da cewa. "Yanzu haka saura wata guda aurena da wani Gambo a garinmu yake shi zai aure ni, kuma ba yaro ba ne 'ya'yansa ma duk sun girme ni. Ga shi an ce matarsa masifaffiya ce, sai dai duk faɗin garinmu shi ne mai rufin asiri. Na fi tsammanin hakan ne ya sa mahaifina ya ba shi aurena." Lokaci ɗaya tausayin yarinyar ya mamaye su, Uwani ta ja hannun yarinyar gefe sannan ta ce. "Ki yi haƙuri iyayenki suna sonki, a tunaninsu turo ki birnin ne zai rage musu wani raɗaɗin rashin da suke ciki. Amma haka za a yi miki aure ko ibada ba ki gama sani ba, shin kin san ma idan aka gama ana yin wanka kuwa?" Yarinyar ta girgiza kai tana faɗin. "Na san dai sallah guda biyar ce a rana, amma ban san me ake faɗa a cikin sallar ba. Ina son na tambayi Aunty me take faɗa nake ganin tana motsa baki idan tana sallah, amma da yake Ladidi dillaliya ta gargaɗe mu da kiyaye abin da babu ruwanmu shi ya sa ban taɓa tambayarta ba." "Innalillahi wa inna'ilahirraji'un." Abin da Uwani da Auta suka iya faɗa kenan, Auta jiki a sanyaye ta ce. "Kuma kin dade da fara fashin sallah?" Ganin yarinyar ba ta gane ba ya sa ta ce. "Ina nufin kin daɗe da fara ganin jinin jikinki." Yarinyar ta gyaɗa kai ta ce. "Eh zan yi shekara uku zuwa huɗu." Uwani da Auta ne suka shiga yi mata bayanin yadda za ta dinga gyara jikinta, don gudun kada ta dinga bari mutane na fahimtar halin da take ciki sannan Uwani ta ɗora da cewa. "Shi wannan wankan da muke yi miki magana a kai ba kamar yadda ake wankan soso da sabulu ba ne, sunansa wankan haila/janaba kuma ya kasaace kala biyu. Akwai siffatul Ijza akwai kuma siffatul kamala. A wankan janaba ta siffarsa ta kamala za ki tanadi ruwa mai tsarki, sai ki karkato da ruwan ki wanke hannunki sau uku. Ki kula! Ba kina zuwa za ki tsumbula hannunki a cikin ruwan ba, sai kin wanke hannunki za ki sake ɗebo ruwan ki wanke al'aurarki tare da ƙudure niyyar irin wankan da za ki yi. Idan wankan haila ne za ki ƙudurta shi, idan na janaba ko na biƙi ne duka za ki ƙudurce niyyarsa. Bayan kin gama za ki ɗaura alwala irin wacce muka koya miki, amma ba za ki wanke ƙafa ba. Abu na gaba da za ki yi sai ki kanfato ruwa da hannunki ki murmurza gashin kanki har sau uku, ki cakuɗa shi sosai yadda ko ina za ji. Sai ki ɗebi ruwa ki wanke jikinki gabaɗaya, sannan kina iya fara wanke ɓangaren dama. Idan kin gama da shi ki wanke na hagu, daga ƙarshe sai ki wanke ƙafarki tun da idan ba ki manta ba mun ce miki alwalar da kika yi a farko ba za ki wanke ƙafa ba." Yarinyar ta jinjina kai cike da gamsuwa. Auta ta ɗora da cewar. "To kin ga wannan shi ne wanka janaba, ki riƙe bayanin sosai domin babu sallah ga wanda ba shi da tsarki." Godiya sosai yarinyar ta yi musu, cikin ƙarfin hali Auta ta buɗe akwatin Shukra ta zaro pad guda uku ta ba wa yarinyar, ta sake jadadda mata muhimmancin tsaftace jiki a lokacin jinin haila. Sallah suka tayar ita kuma yarinyar ta fice domin gyara jikinta, tana mamakin irin duhun jahilcin da ta dinga aikatawa a baya. "Maganar gaskiya iyaye da yawa sai sun tsaya a gaban Ubangiji, ki duba ki ga yarinya kusan shekara goma sha bakwai amma ba ta san yadda za ta aiwatar da ibada a karan kanta ba?" Auta ta yi maganar a lokacin da suka ƙarasa can reception, Uwani ta sauke ajiyar zuciya ta ce. "Gaskiya dai kam da matsala, abin takaicin ma wai wani can tsoho mai mata za a aura mata. Kuma a ɓangaren iyayen aikin nasu su ma suna da laifi wallahi, yaro ko ba kai ka haife shi ba atleast ka ba shi ilimi ko iya na addini ne. Ki duba fa ki gani, sallah wannan ba ta gama sanin yadda ake yin ta. Allah Ya kyauta." Uwani ta ƙarasa maganar tana tsaki. Kiran Aunty ne ya shigo tana tambayar jikin Shukra, sannan ta ce Uwani ta kwatanto mata asibitin za ta ƙaraso idan ya so su sai su koma gida. Shukra na zaune ta fara jin ƙasan mararta da bayanta yana ci gaba da karta mata, sannu a hankali take jin ciwon na ƙaruwa. Lokaci ɗaya wani gumi ya shiga karyo mata, jin zafin ciwon ya sa ta katse video call ɗin da suke yi da Salim wacce suka shafe sukan awa guda suna hirar soyayya. A daidai wannan lokacin ne Dr ya shigo, sai da ya yi wa Shukra sannu sannan ya ƙarasa wurin ɗayar matar don ta galabaita sosai. Safar hannu ya sa ya duba matar sannan ya ce. "Sannu kin ji, kina gab da sauka In shaa Allah nan ba da jimawa ba." A wahalce matar ta ɗago shanyayyun idanunta ta ce. "Dr ni dai don Allah ka yi mini CS ko na huta da wannan wahalar." "Yanzu haka kina 8cm fa In shaa Allah nan ba da jimawa ba za ki iya sauka. Zan turo nurses yanzu idan na fita, za su tsaya a kanki." Ba ta iya amsa masa ba don saboda zafin ciwo komai da kowa ma haushinsa take ji. Gaban gadon Shukra ya ƙarasa, a lokacin da ya tsaya ta jiƙe sharkaf da gumi. Ga man da aka lafta mata a wurin gyaran kai sai gangaro mata yake yi, tun da ya ƙarasa ya cire safar hannunsa ya sauya wata take bin sa da harara a fakaice. "Hajiya kwanta zan duba ki." Shukra ta watsa masa harara ta ce. "Ka yi mini uwar me? An gaya maka ni ma shegiya ce da zan zauna wani ƙato ya gane tsiraicina?" Safar hannunsa Dr Hussain ya zare ba tare da ya tanka mata ba, ya saki murmushi sannan ya fice daga ɗakin. Yana fita Shukra ta bi shi da harara ta ce. "Don Allah dube shi kamar wani mutumin arziƙi ashe ƙwallan ɗan iska ne." Fitar Dr babu jimawa wani azababban ciwo ya baƙunci Shukra, a galabaice ta fisge ɗan kwalin kanta haɗe da ribon ɗin ta yi wurgi da shi. Cikin azaba ta dafe baya tana faɗin. "Ya hayyu ya ƙayyum, wash! Wayyo bayana zai ɓalle." Ana cikin haka sai kakar matar da suke ɗaki ɗaya da ita ta shiga, da yake gadon Shukra daga bakin ƙofa yake. Sai da ta yi wa Shukra sannu sannan ta ɗago jarkar hannunta tana faɗin. "Halima ga tofin nan na karɓo miki maza ki ɗaga kanki ki shanye, cikin ikon Allah an ce kina sauke robar sai haihuwa." Dattijuwar na gama magana tana shirin ƙarasawa gaban gadon jikar tata, Shukra ta fisgo jarkar da sauri cikin jin zafin ciwo ta murɗe murfin ta ɗaga kai tana ɗaɗɗaka. Da sauri Dattijuwar ta warto jarkar da tuni Shukra ta kusa shan rabi, ganin haka ya sa Shukra ta fashe da kuka mararta na karta mata ta ce. "Iya don Allah ki ban na shanye na haihu yanzu na huta." Dattijuwar ko ta kan Shukra ba ta bi ba ta miƙa wa Halimatu ta ɗaga kai ta shanye. Nurses ne suka shigo kuma a wannan lokacin ne jaririn Halimatu ya faɗo, da sauri suka shiga hidimar gyara ta da jaririn da ta haifa. Ana cikin haka sai ga Dr Hussain ya shiga, Shukra na ganinsa ta fisgo hannunsa har sai da ya kusa faɗuwa kanta. Ta yi shame-shame a kan gado ta wara ƙafafu tana faɗin. "Don Allah zo ka duba ni Dr, ni ka cire mini jaririn ma gabaɗaya na huta." Dr Hussain ya yi murmushi ya ce. "A'a Hajiya ai ni 'yan iska kawai nake dubawa ke da ba 'yar iska ba..." Da sauri Shukra ta katse shi. "Wallahi Salim shi ne babban ɗan iska Malam Dr, don Allah Malam Dr ka zo ka duba ni." Shukra ta ƙarasa maganar tana fusge zanin jikinta. Dr Hussain na duba ta ya ga ta kai 5cm don haka ya ce mata ta yi haƙuri ita ma tana gab da haihuwa, ban da gyaɗa kai babu abin da take yi. Shukra tana haɗa ido da kakar Halimatu ta ce. "Iya don Allah kada ki sake haihuwa, wallahi haihuwa mutuwa ce." Dattijuwar ta ƙumshe dariyarta ta ce. "Yarinya ni kuwa tsofai-tsofai me zai haɗa ni da haihuwa?" Runtse ido Shukra ta yi tana jin wani zummm a ƙasan mararta, sai da ta yarfe hannu sannan ta sake cewa. "Wai Iya kin san ma me ake nufi da haihuwa? Wayyo marata!" Dattijuwar ta ce. "Yar nan ina zan san haihuwa tun da ta zo kan 'yan zamani." Ta yi maganar tana sakin murmushi sannan ta fice daga ɗakin. Kafin wani lokaci tuni an gyara Halimatu da ɗanta har an sauya mata ɗaki, abin duniya goma da ashirin ya sake rufe Shukra ga Nurses ɗin sun ƙara duba ta sun ce ta ɗan jira da saura haihuwarta. Uwani na gama kwatantawa Aunty asibitin ta dubi Auta ta ce. "Auta mu leƙa mu ga halin da Aunty Shukra take ciki don..." Auta ta katse ta da sauri. "A'a Uwani kedai ki shiga wallahi ba zan iya shiga labour room ba tsoro gare ni." Uwani ta miƙe ta nufin ɗakin da Shukra take ciki. Tun daga bakin ƙofa ta fara jiyo ihu da salatin Shukra, da sallama ta shiga ɗakin tana shiga ta ci karo da ɗankwalin Shukra a bakin ƙofa. Gashin kanta duk a hautsine ta yi zuru-zuru, jiki a sanyaye Uwani ta ce. "Sannu Aunty Shukra!" Don yanayinta ba ƙaramin tausayi ya ba wa Uwani ba. "Uwani ina Salim?" "Wai Babynki?" Uwani ta faɗa, takaici ya sake rufe Shukra ta ce. "Ke da babyn na ci banten ubanku! Wallahi ki je ki ce masa idona idonsa sai dai wani ba shi ba." Uwani duk yadda take cikin jamami sai da ta saki mutmushi, ganin haka ya harzuƙa Shukra ta ɗauki jakarta ta wurga mata. A guje Uwani ta fice tana dariya, don abin na Shukra abin tausayi abin kuma ban dariya. Tana tafe kiran wayar Jafar ya shigo mata, baki ɗauke da sallama ta ɗauka. Bayan sun sake gaisawa ya tambaye ta jikin Shukra, Uwani na shirin ba shi amsa daga bayanta ta ji alamun gudu da ihun Shukra tana faɗin. "Wayyo Allah jama'a!" A guje Uwani ta ƙara gaba don ta ɗauka wani abin ne ya koro Shukra daga ɗakin, ganin gudun da Uwani da Shukra ke yi ya sa wasu mata masu ciki su biyu, wani magidanci, Salim sai kakar Halimatu suma suka ɗiba a guje suka yi gaba. "Jama'a kowa ya yi ta kansa ga haihuwa nan tana bin maza da mata, wayyo Allah! Haihuwa ta kawo mini farmaki." A wahalce Shukra ta ƙarasa reception a daidai wannan lokacin wani Alhaji na tsaye ta ƙarasa wurinsa ta cikwikwiyo rigarsa ta ce, "Dr zo ka zaro mini ɗan nan ko hannu ko ƙafarsa ka samu ka fisgo shi ko na huta." Da sauri mutumin ya kawar da kansa gefe ganin Shukar daga ita sai doguwar rigar atamfa, kai ba ɗankwali sai pant ɗin da ta ɗora a kanta a madadin ɗankwali. "Subhanallah hajiya ni ba likita ba ne." Alhajin ya furta cikin muryar ustazai. "Ƙarya kake ba kai ne ka duba ni ɗazu ba? Wallahi mu je sai ka haife mini cikin nan. Ko kuma ka mayar mini da naƙudar." "Wa'iyazubillah, subhanallah ina Nurses ku zo ga mai laruri ta yi dama da ni, kuma subhanallah ta kasance ba muharrma ta ba." A daidai wannan lokacin Nurses suka ƙaraso suka kamata, suka wuce da ita ɗakin da take tana tafe tana ɗingisa ƙafa. Da sauri Aunty ta ƙarasa ɗakin Shukra, don shigowarta babu jimawa ta hango an wuce da ita. "Hajiya wace ce ke?" Ɗayar Nurse ɗin ta tambayi Aunty. Aunty na shirin magana Shukra ta ce. "Mahaifiyata ce, wallahi uwarmu ɗaya ubanmu ɗaya da ita." Jin haka ya sa suka ƙyale Aunty ta shiga a fili suka dinga murmushin soki-burutsun Shukra, suka sake duba Shukra a wannan lokacin har ta kai 8cm. Bayan sun gama duba ta suka fita Shukra ta fara ihu. "Shukra ki dinga salati kina addu'a kin ji In shaa Allah, Allah zai raba ku lafiya." "Don Allah Aunty kada ki haihu, wallahi ganin idona yau na ga haihuwa na kawo mini farmaki." Aunty ta yi murmushi ta ce, "To shi kenan Shukra ba zan haihu ba." Shukra ta ja hannun Aunty tana ƙoƙarin kai mata shi ƙasanta ta ce, "Don Allah ki fisgo jaririn nan ko na huta Aunty. Wayyo bayana wayyo marata, ya Allah ka mayar da cikin nan jikin Salim. Allah ka sa shi ma cikin nan ya fito masa ya haife shi, wai Aunty ko ke zan ba wa cikin nan ki haife mini?" Aunty ce ta shiga kwaɓar ta tana nusar da ita addu'o'in da ya da ce ta yi, lokaci ɗaya ciwon ya taso mata gadan-gadan da sauri Aunty ta fita ta kira Nurses ɗin, shigowarsu babu wuya Shukra ta haifo jaririyarta mai tsananin kama da Salim. Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 idan littafi ya kammala cmplt 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *DoctorMaryamahGraphics and Data Services.* MTN •1gb ₦300 •2gb ₦600 •3gb ₦900 •5gb ₦1500 AIRTEL 1gb ₦350 •2gb ₦700 •3gb ₦1.050 •5gb ₦1.750 Glo •1gb ₦300 •2gb ₦600 •3gb ₦900 •5gb ₦1500 9mobile 1gb ₦350 •2gb ₦700 •3gb ₦1.050 •5gb ₦1.750 Our Services:- •Data Bundles •Airtime purchase •Cable TV subscriptions •Recharge card •Electricity Bills payment •Converting Airtime to cash •WAEC, NECO and jamb pins Make payment into:- 3195402912 Firstbank Maryam Ibrahim 8136402046 Opay Maryam Ibrahim Send the receipt into:- +234 701 714 8194 Available 16hours📌 from 6am to 10pm. And All types of different Logo invitation card and vide, save the Date and more_____ For more info:- 08136402046 Ba a ɗauki lokaci ba Nurses suka gyara Shukra da jaririyarta, Aunty ban da murmushi babu abin da take yi. Ta ƙura wa jaririyar ido cikin ranta tana harsashen nan da ɗan wani lokaci ita ma tana nan ɗauke da ɗanta ko 'yarta. Da kanta da fita ta nuna wa su Uwani jaririyar sai a lokacin Salim ya ƙarasa, a daidai lokacin ne kuma Hajiyar Salim da yayarsa Aunty Khadija suka ƙaraso. Salim ban da sakin murmushi babu abin da yake yi, nan take suka shiga ɗaukan jaririyar hoto. Auta ta ɗauki waya ta kira Mami ta sanar da ita, tana shirin kiran Daddy ya sauri Aunty ta katse. "Auta ba za ki riga ni isar da sakon zuwan kishiya ba, ni zan kira Daddy da kaina na sanar da shi." Uwani ta saki murmushi sannan ta ce. "Ni ma bari na kira Nur na sanar da shi zuwa baby, kai bari ma na kira shi Video call." Da yake a yanzu sunan da Uwani ke kiran Jafar da shi, shi kuma yana kiranta da bakin tsiwa ko ya ce mata Jidda. Daddy ba ƙaramin farinciki ya yi ba, a ɓangare ɗaya ya jinjina mutumcin da karamcin Aunty duk irin zaman doya da manjar da suke yi ita da Mami, hakan ba sai ta watsa wa jininta ƙasa a ido ba. Nan take ya ce musu zai ƙaraso asibiti, kafin ya kashe wayar ya yi wa Aunty tukwici mai tsoka. Kafin wani lokaci tuni labarin haihuwar Shukra ya watsu daga danginta har zuwa dangin Salim. Da yake Shukra an sha ruwan zafi sai baccin wahala take sha, saboda dare ya yi a lokacin da ta haihu don haka likitocin suka ce sai da safe za su sallame ta, don su ƙara ganin kyawun jikinta da na jaririyarta. Aunty ce ta kwana a wurinta, Auta da Uwani suka koma gida. Uwani ta girka abinci Auta ta kawowa su Aunty da ruwan zafi, gabanin su Uwani za su fita daga asibitin ne kuma Madina ta ƙarasa da yake ranar tana da lectures sai bayan da aka yi haihuwar aka sanar da ita. Tun da Shukra ta ga irin ɗawainiyar da Aunty take yi da ita da jaririyarta jikinta ya fara sanyi, game da irin rashin mutumcin da ta dinga yi mata a baya. A daren ranar jaririyar kwana ta yi tana rigima, amma Aunty ta ce Shukra ta kwanta ta yi bacci bayan ta ba ta mama ta sha, ita ta ci gaba da kula da ita. Washegari da sassafe sai ga Mami ta dira a asibitin, ko da ta shiga ɗakin da Shukra take sallama kaɗai ta yi wa Aunty amma ko ya me jego ba ta ce mata. "Shukra yanzu me yake damunki? Babu dai wani abu da kike buƙata, don kin san wani abin dole sai uwa ce za ta yi maka shi." Mami ta furta a gadarance, Aunty ta ji zafin maganar amma sai ta yi kamar ba ta fahimci zancen Mami ba. Ta danna wayarta ta kira Daddy tana faɗin. "Ranka ya daɗe na fa turo maka hoton amaryarmu na Good morning, ni sai da na turo maka ma na ce an ya wankanta ba zai ƙwace mana kai ba." Aunty ta ƙarasa maganar tana ajiye jaririyar a kan cinyar Mami ta fita ta ba su wuri, ta yi haka ne domin kada Mami ta lura maganarta ce ta ba ta haushi har ta fita. "Mami gaskiya abin da kika yi bai kamata ba, matar nan mene ne ba ta yi mini ba? Tun fa jiya take wurin nan ko motsi na yi sai ta ce ko akwai abin da nake buƙata, kuma idan ina so nan take za ta yi mini yanzu kuma ki faɗi haka? Ni wallahi yanzu ma kunyarta nake ji a kan abubuwan da na yi mata a baya, wallahi na fahimci mutumiyar kirki ce..." "Ke dalla rufe mini baki." Mami ta katse Shukra a zafafe. "Ai kin haihu yanzu gani kike matsayinmu ɗaya dole ki faɗa mini abin da ranki ya so, sakarai shashasha. Maƙiyinka dama yana sauyawa ne ban da haukanki?" Shiru Shukra ta yi ta tura baki gaba tana jin babu daɗi akan abin da mahaifiyarta take faɗa. Koda aka sallame su zuwa gida Aunty ba ta fasa duk wani abin kyautatawa da take yi wa Shukra ba, don hatta wanka ita take yi mata duk da ba wankan ganye ba ne saboda likitoci sun ce kada ta yi da shi don yana iya kawo hawan jini. Da yake a wannan lokacin Safna ta dawo daga India haka ta haɗo wa Shukra kayan barka akwati guda, kayan jaririya kala-kala kallo ɗaya za ka yi musu ka tabbatar da an watsa narkakkiyar dukiya a ciki. A haka lokaci ya ci gaba da gangarawa har aka yi suna, yayin da yarinya ta ci sunan Hajiyan Salim wato Nauwara. Kwanan Shukra goma ciff Daddy ya ce ta koma ɗakinta, a cikin danginta ne Mami ta samo wacce za ta ci gaba da zama da Shukra a gidanta. Bayan da aka yi suna ne ita kuma Aunty laulayi ya saka ta a gaba, har ya zamana duk ranar gidanta sai dai Auta da Uwani su yi abinci. Saboda wani lokcin da ta ji ƙamshin girkin za ta fara kwara amai, tuni Auta da Uwani suka ranfo Aunty. Sai dai Auta na son sanar da Mami tana tsoron faɗanta, saboda haka ta ja bakinta ta kulle. Sannu a hankali Mami ta fahimci halin da take ciki, a lokacin hankalin Mami ba ƙaramin tashi ya yi ba. Ita dai ci wa kanta alwashin ba za ta taɓa zuwa wurin wani malami ta kai kukanta ba. Amma duk hanyar da za ta bi cikin makirci da tuggu ta ƙudurta a ranta sai ta bi ta salwantar da cikin jikin Aunty. Ginin gidan da Daddy ya sa ake yi wa Jafar ba ƙaramim nisa ya yi ba, duk wata sai ya turo da kuɗi domin a ci gaba da aiki. Sai dai shi a tsammaninsa wurin zaman mace ɗaya ne, amma tun asalin fitar da famdisho Daddy ya sa aka fitar da tsarin zaman mace biyu. Hatta Mami ba ta san da wannan tsarin ba, abu ɗaya Mami ta dage a kansa shi ne haɗa kayan lefen Safna. Don ta yi lefe na bajinta har wani filinta ta sayar ta haɗa ta sayo wasu danƙara-danƙaran lesuna. Su Uwani hada-hada suka shiga ta saukar Alƙur'ani da za su yi, tare da Candy sai dai tarazar kwana biyu ne a tsakani. Ranar Laraba suka yi candy yayin da suka yi bikin sauka ranar juma'a. Ɗalibai da yawa ne suka yi sauka aka raba musu kyaututtuka gwanin birgewa. Duk wanda ya halarci taron sai da su Uwani suka birge shi, bayan wani lokaci kowa ya watse suka wuce gida aka shiga gudanar da walima. Auta da Uwani tamkar tagwaye haka suka yi anko aka yi musu kwalliya gwanin birgewa, saboda wanda bai sansu ba idan ya gan su zai yi tsammanin ciki ɗaya suka fito. Domin ta ɓangaren kamanin suna yanayi sakamakon Uwani na fisgar kama da Daddy, kuma dama mahaifinta, baba Inusa da Daddy duk sun fi kama a cikin 'ya'yan Dada. Maryama mahaifiyar Uwani takanas ta sa aka kawo wa Uwani da Auta tinkiya da rago a cikin awakin da take kiwo, lokacin da Daddy ya gani ya ji daɗi amma sai ya ce da ta ba su koda tinkiya ce a yanka musu, a yi sadaka ba sai ta haɗa da rago ba amma ta ce dama can ta ƙudurta haka a ranta. Ta shiga yi wa Daddy godiya bisa jajircewar da ya yi a kan tarbiyya da ilimin Uwani, sai da Daddy ya gama sauraronta ya ce. "Maryama ki daina yi mini godiya domin duk abin da na yi wa Uwani kaina na yi wa. Allah Ya jiƙan Umaru na tabbata yau ko ni na mutu na bar masa iyalina ba za su yi kukan rashina ba, Allah Ya gafarta masa halinsa na gari ya bi shi." Wani abu ta ji ya tsarga mata, musamman da ta tuna kyawawan halaye da ɗabi'unsa. Idanunta suka ciko da ƙwalla jiki a sanyaye ta ce, "Amin Ya Rabbi Yaya, Allah Ya ƙara girma Ya shirya zuri'a." Daddy ya amsa da Amin. Lokacin da su Uwani suka yi candy cikin Aunty kusan watansa takwas, a wannan lokacin kuma Jafar saura wata ɗaya ya dawo gida Najeriya. Bayan kwana biyu da candy ɗin su ne kuma Dr Bilal ya turo manyansa aka saka ranar aurensa da Auta shekara ɗaya, ita kuma Madina an kawo kuɗi amma ba a tsayar da rana ba, saboda saurayinta gini yake yi sai ya kammala za a tsayar da lokacin biki. Tun da Jafar ya faɗi lokacin dawowarsa Uwani take lissafi zuciyarta fes, don idan ta ce ba ta yi kewarsa ba ta yi ƙarya. Haka kawai idan ta zauna ta tuno irin faɗan da suke da cin zalin da yake yi mata sai ta saki murmushi. A ɓangaren Safna ma zuciyarta fes don ta san Jafar yana dawowa za a ɗebi kwanaki a sha bikinsu, ita kanta Mami burin da take ci kenan. Sai dai Uwani da ta tuna maganar auren Jafar sai ta ji duk jikinta ya yi sanyi, musamman da ta tuna kalamansa na baya da yake faɗa mata cewar Safna ita ce zaɓinsa. Tun satin da Jafar zai dawo Aunty ta fara yi wa Uwani dafe-dafe da tsimi kala-kala waɗanda ta saya a wurin BOJUWA HERBAL'S&SCENTS 08032773332, saboda yadda ta yarda da ingancinsu domin a wurinta take sayan kayan gyara da magungunan sanyi kala-kala. A ranar da Aunty ta saka Uwani ta a ɗaki ta ba ta wani dafaffan tsimi kurɓa ɗaya ta yi ta ce. "Aunty ni fa wannan abubuwan wallahi ba wani amfani da za su yi mini, kawai dama ba ki kashe kuɗinki ba." Riƙe da baki Aunty ke kallon Uwani don ta san a wannan lokacin dai Uwani ta gama mallakar hankalin kanta. "Me ya sa kika ce haka? Ko sakarcin naki za ki yi mini?" Aunty ta tambaye ta tana haɗe fuska. "To Aunty ni fa babu wani abu da ya taɓa haɗa mu..." Da sauri Aunty ta zaro ido waje, ta ɗora kofin a kan mudubi tana salati. "Uwani ki gaya mini gaskiya ba na son shashancin banza." A kunyace Uwani ta ce. "Allah ni fa da gaske nake." Jinjina kai Aunty ta yi sannan ta miƙa mata kofin da wata gumba ta ce. "Maza ki shanye shi ki ba ni kofin an jima za mu zauna da ke. Don na lura Uwani sai na cire fuskar Auntyn na ajiye a gefe na yi miki lecture mai zaman kanta sannan za ki dawo daidai." Uwani ta fara shan tsumin tana yatsina fuska don ko kaɗan ba ta ji daɗinsa ba. Kusan kullin da dabarun da Aunty ke koyawa Uwani na sace zuciyar miji, tun Uwani na jin nauyin Aunty har ta ware wani abin ma take yi mata tambaya idan ba ta gane ba. Ana saura kwana uku Jafar zai dawo aka yi wa Uwani gyaran jikin dilka da halawa, washe gari aka yi mata lalle da gyaran gashi. Auta ban da tsokanarta babu abin da take yi, Mami kuwa zuciyarta a cunkushe take ganin yadda Uwani ta sauya ta yi wani shar tamkar sabuwar amarya. A ranar da Jafar zai dawo hatta Aunty sai da ta taya Uwani tsara masa abinci, bayan soye-soye har da abin da ya danganci gashi a oven. Wani tsalalelen leshi Uwani ta saka doguwar riga, ta naɗa ɗaurin ɗaukwali sai ga ta fito tamkar a sace ta. "Malama wannan wankan a rage shi don wallahi kada ki sumar mini da ɗan uwa, na rantse da Allah idan ya ga wannan wankan sai kin susutar da shi!" Auta ta raɗa mata a kunne. Uwani ta yi farr da ido ta ce, "Yarinya ai yau sai dai ki runtse idonki don kada su ƙone ƙurmus, kin san dai shekara guda har da rabi ba banza ba..." Kalaman Uwani suka maƙale sakamakon jin horn ɗin motar Daddy. "Bari mu ja gefe mu ga kallon masoya, inyeeee yau ango ya dawo." Auta ta faɗa cikin sigar tsokana. Uwani sai murmushi take a ɓangare ɗaya wata irin kunyar Jafar take ji ta lulluɓe, tana daga barandar ɗakin Aunty ta hango fitowarsa daga cikin mota. Wani irin kwarjini ya yi mata, ya ƙara haske sosai da 'yar ƙiba kaɗan. Ga wani saje da ya tara ba ƙaramin birge ta ya yi ba. Tana yawan mamaki idan ya turo mata hotuna ko idan suna video call, na yadda ya sauya sai a fili ta sake tabbatar da haka. "Idan kin gama leƙen malama ki fito habibinki yana babban falo." Aunty ta faɗa tana dafa kafaɗar Uwani, kunya ce ta kama Uwani a ɗan kunyace ta ce. "Wallahi Aunty kunya nake ji." Sakin baki Aunty ta yi ta ce, "Sai ka ce wacce za a kai ɗakin miji yau? Uwani wallahi kika sake kika zubar da huɗubar da na yi miki sai ranki ya ɓaci." Uwani ta yi murmushi Aunty na gaba Uwani na biye da ita a baya. Shigarta falo ya yi daidai da ɗagowar idabuwansa da suke a yunwace da son ganin ƙwayar idonta, sakamakon jin wani yalwataccen ƙamshin turarenta da ya doki hancinsa. Ya yi matuƙar kewar bakin tsiwarta. Uwa-uba gabaɗaya kyakkyawar fuskarta. Uwani ta sunkuyar da kai ƙasa, a kunyace ta zauna su Daddy sai jan jafar da hira suke yi ana hirar yaushe gamo. Amsa yake ba su amma hankalinsa yana kan Uwani da take jin ta gabaɗaya a takure. Mami kuwa da gayya ta dubi Jafar ta ce. "To Jafar wai-wai dai ta ƙare, yanzu sai a zo a saka rana tun da kayan lefe sun kammala kai ma kuma ka dawo gida." Ƙirjin Uwani ya buga dam! Jafar ya ɗan sosa kai a duburburce ya ce. "Ammm... eh dama... na ce dai sai... an kwana..." "Ai kuwa rannan Uwani take ce mini tana son fitar da ankon wuni, ni leshi ne ko atamfa Uwani?" Aunty ta tsinci kanta da furta haka, don ba ta son Mami ta gane lagon Uwani a ɓangaren kishi. Sai da Uwani ta haɗiyi yawu mai ɗaci ta saki murmushin yaƙe ta ce. "Leshi ne Aunty amma ni ya yi mini arha ina jin mu sauya wani." Uwani ta yi ƙarfin halin faɗar haka. Sam Mami ba haka ta so ba, Jafar ya kafe Uwani da kallo ƙirjinsa na bugawa. "Yarinyar nan kenan ko kishina ba ta yi da har za ta fitar da anko? An ya ba ni kaɗai nake kiɗa da rawata a kanta ba?" Jafar ya ayyana a ransa. "Jafar ya kamata ku ƙarasa sashenku ka yi wanka ka huta ko?" Daddy ya katse shirun. Yana gama magana, Mami ta shige ɗaki fuuuu Daddy ya saki murmushi don ya fahimci salon Mami tun farkon maganarta, da yadda Aunty ta sauya akalar maganar. Hanyar fita ya nufa Aunty da Daddy kowanne ya shiga sashensa, Uwani ta yi saurin bin Aunty idanunta sun ciko da ƙwalla. "Au abin da take son aiwatarwa a kanku kina nufin za ki ba ta dama ta yi nasara a kanki ne? Bari ki ji, sirikarki da biyu ta tsiro maganar auren Jafar saboda ta lalata farincikin da kuke ciki. Maza ki goge hawayenki ki wuce ki tarairayi mijinki don na san ya yi kewarki, kuma saura anjima na ga ƙafarki a nan don ko Auta na ce ita da shiga sashenku sai bayan kwana uku. Na san kafin lokacin an gama cin amarcin..." Uwani ba ta gama jin maganar Aunty ba ta fita da gudu saboda kunya, lokacin da ta sauka tuni har ya shiga sashensu. Tana shiga falon ganin baya ciki ta fara waige alamar nemansa, ta baya ta ji ya rungumota kusan lokaci ɗaya suka sauke ajiyar zuciya. Jafar ya cusa kansa cikin wuyanta ya fara sakar mata kisses, cikin tsantsar soyayya da kewarta. "Ya Jafar!" Uwani ta furta cikin wata irin murya. Bai amsa mata ba sai ma ƙira tura kansa da ya yi cikin wuyanta yana shaƙar ƙamshin turarenta, a hankali ya juyo da ita suna kallon juna ta yi saurin sunkuyar da kai ƙasa. "Laifin me na yi da ba a yi mini sannu da zuwa ba?" Uwani ta yi murmushi ta ce, "Ni fa kunyar su Daddy na ji." Bin ta yake da kallo yana mamakin sauyinta, komai na Uwani ya sauya tamkar ba ita. "Bakin tsiwa kin ƙara girma!" Da sauri ta cusa kanta a ƙirjinsa ta ce. "Ni fa ba na so wai ƙare mini kallo ka yi dama." Jafar Ya shafo fuskarta ya ce. "Da gaske komai na ki ya sauya, sai dai ban sani ba ko halinki na ƙiriniya da tsiwa yana nan?" Uwani ta saki murmushi a ranta ta ce. "To dama mai hali yana fasa halinsa ne?" A fili kuma ta ce. "Ya Jafar ga ruwan wanka fa ya kamata ka yi wanka ka huta." "Mu je ki taya ni..." Ganin yadda Uwani ta zaro ido waje haɗe da ja baya ya katse maganarsa yana dariya. "Na ga alamar kunyar nan za ta hana ni rawar gaban hantsi dai, amma zan yi maganinta." Uwani tana ji ba ta tanka masa ba, Jafar ya shiga ɗaki ya rage kayan jikinsa. Lumshe ido ya yi yana shaƙar ƙamshin turaren don ba ɗaramin daɗi ya yi masa ba. Kiran Safna ne ya shigo wayarsa, da sauri ya saka wayar a silent sannan ya tura mata sakon yana zuwa daga ƙarshe ya kashe wayar gabaɗaya. Bayan ya yi wanka ƙaramar riga ya saka da wando 3 quater, a falo ya samu Uwani tana zaune tana ganinsa ta sakar masa murmushi sannan ta fara zuba masa abinci. A kusa da Uwani ya zauna ya shagwaɓe fuska yana faɗin, "Na yi kewar girkin nan na ki." Murmushi ta sakar masa Jafar ya buɗe baki, a kunyace Uwani ta fara saka masa yana ci har ta ɗan saki jikinta. Sannu a hankali shi ma yake ba wa Uwani suna ci yana ba ta labarin irin gwagwarmayar da suka sha. Wani irin tausayinsa ya kama ta, ta shafo gefen fuskarsa ta ce. "Amma me ya sa ba ka dawo gida ba Nur?" "Ai duk wanda kika ga ya tafi babu damar ya dawo matuƙar ba rashin lafiya ce ta kama shi ba, ita ma sai wacce ta ci ƙarfinsa. Yanzu ba ga shi na dawo ba, kuma wani abin farin cikin ma a Kano zan ci gaba da aiki In shaa Allah." Cikin farinciki Uwani ta ce, "Kai amma wallahi na yi farinciki." A haka suka ci gaba da hira kuma sannu a hankali hirar tasu ta fara sauya salo, haka kawai Uwani ta tsinci kanta cikin faɗuwar gaba "Nur ba za ka leƙa wurin Mami ba ko za ku yi hira." Uwani ta furta a ɗan tsorace. Har cikin jikinsa yake jin faɗuwar gaban Uwani, ya marairaice murya don ya fahimci halin tsoron da take ciki ya ce. "Ko Mami ai za ta yi mini uzuri yau, ta san fa na yi kewar matata, don haka ni yau angoncina na baya zan fanshe." Idanu Uwani ta waro waje, Jafar ya ɗaga mata gira yana kashe mata ido ɗaya. Dukan wasa ta kai masa tana faɗin, "Ni gaskiya ban yarda ba." Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 Idan littafi ya kammala 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *DoctorMaryamahGraphics and Data Services.* MTN •1gb ₦300 •2gb ₦600 •3gb ₦900 •5gb ₦1500 AIRTEL 1gb ₦350 •2gb ₦700 •3gb ₦1.050 •5gb ₦1.750 Glo •1gb ₦300 •2gb ₦600 •3gb ₦900 •5gb ₦1500 9mobile 1gb ₦350 •2gb ₦700 •3gb ₦1.050 •5gb ₦1.750 Our Services:- •Data Bundles •Airtime purchase •Cable TV subscriptions •Recharge card •Electricity Bills payment •Converting Airtime to cash •WAEC, NECO and jamb pins Make payment into:- 3195402912 Firstbank Maryam Ibrahim 8136402046 Opay Maryam Ibrahim Send the receipt into:- +234 701 714 8194 Available 16hours📌 from 6am to 10pm. And All types of different Logo invitation card and vide, save the Date and more_____ For more info:- 08136402046 Murmushi Jafar ya saki sannan ya miƙe tsaye yana faɗin, "Naki wasa ne yarinya, yanzu dai ɗauko mayafinki za mu fita shopping." Da sauri Uwani ta miƙe tana cewa. "Bari na kira Auta mu tafi tare." Ba ta jira cewarsa ba ta ɗauki mayafinta ta wuce sashen Daddy. Lokacin da su Uwani suka fito Jafar na jikin motar Daddy suna magana da shi, sai a lokacin Auta ta lura da fuskar Uwani ta gimtse dariyarta da hannu ta ce. "Wai ni duk cikin ƙaunar ce aka goge miki wannan jan bakin ne?" Uwani ta wurga mata harara tana tuna lokacin da Jafar ya shammace ta ya fara sakar mata kisses, har sai da ta kwace kanta da ƙyar. Ta dubi Auta ta ce, "Wallahi Auta ki kiyaye ni kin saka mana ido ni da mijina, wai ma me kike nufi?" "Me kuwa nake nufi? Ga abin da nake nufi can a gefen kumatun mijinki!" Auta ta faɗa tana nuna Jafar, zaro ido waje Uwani ta yi ganin janbakinta danɓar a gefen baki zuwa kumatunsa, don ma ta lura kamar Daddy bai gani ba tun da ba ta ɓangare yake ba. "A toh ki ja shi gefe ki goge ragowar kar mu fita a dinga yi masa dariya." Uwani ta kwaɓe fuska kamar za ta yi kuka, lokacin da suka ƙarasa gaban motar Daddy ya wuce sashensa. Sam Jafar ya manta da Auta, Uwani ta saka hannu ta fara goge masa gefen kumatunsa ta ce. "Nur duk ka ɓata gefen bakinka da janbaki fa." Janyota ya yi jikinsa ya rungume ta, yana jin soyayyarta har cikina jikinsa, a ɗan kunyace Uwani ta raɗa masa. "Auta fa tana gefenmu!" Shi ma Jafar ya mayar mata da cewar, "Auta za ta hana ni soyayya da matata ne? Ko a gaban Daddy tsaf zan rungume ki." Uwani ta janye jikinta tana dariya ta ce. "Wallahi da ka kashe ni da kunya." Zagayawa Jafar ya yi ya shiga mota, Auta ta mintsino Uwani ta ce. "Idan kun san iskanta ni za ku yi Uwani sai na koma inda na fito, haka kawai ku sa Autar Daddy a gaba kuna falsafar ɗiban albarka." Uwani ta saka dariya tana shigewa Mota. Suna fita daga gidan kai tsaye Jafar ya wuce da su babban kantin Binafa shopping Complex da ke kan titin rijiyar zaki, saye-saye kala-kala ya yi musu dangin kayan ƙwalam da maƙwalashe. Sannan ya biya ya saya musu shawarma, burger da gasassun kaji. Bayan haka ya tambaye su ko akwai abin da suke buƙata, gabaɗaya suka ce babu saboda dama kayan zaƙi ne zaɓinsu kuma ya riga da ya saya musu. Lokacin da suka dawo gida kusan goma saura, a gate ya miƙa wa Auta ledojinsu ya ce ta kaiwa Mami da Aunty kowa da tashi. Uwani ta fakaici idon Auta ta sakar mata gwalo sannan suka wuce sashensu. A falo Jafar ya baje musu ledojinsu, Uwani kuma ta faɗa toilet ta yi wanka. Bayan ta fito ta saka wata doguwar riga mara nauyi, ledar kaza ta fara janyowa ta saka a faranti tana faɗin. "Kasan dai ni a nan fa na fi kauri Nur, da hajiya dajaja zan fara." Murmushi Jafar ya yi ya saka hannu ya dinga bata yana ci, suna hira cikin so da ƙauna. Sai da suka ci suka ƙoshi sannan Jafar ya ce Uwani ta ɗauro alwala za su gabatar da nafila. Jiki a sanyaye Uwani ta ɗauro alwala, bayan ta fito shi ma Jafar ya ɗauro alwala. Jafar ya jima yana addu'o'i a lokacin da suka idar da sallah, sannan ya dafa kanta ya sake karanto addu'a. Bayan ya gama addu'o'in ya kama Uwani ya fara rage mata hijabin jikin, duk tsiwa da bakin Uwani tuni bakinta ya mutu. Jikinta ban da rawa babu abin da yake yi uffan ta gagara faɗa. Jafar ya lura da yanayin Uwani don har a jikinsa yana jin bugun zuciyarta, don haka lokacin da ya janyo ta jikinsa ya ce. "Tsoron me kike ji?" A kunyace Uwani ta sunkuyar da kai ta ce, "Ba komai Nur." Murmushi ya sakar mata a hankali hannuwansa suka fara yawo a jikinta, dalilin da ya sake birkita shi cikin yanayi marar misaltuwa. Jin yana aika mata baƙin saƙwannin da bai taba ratsa inuwarsu ba ya sa jikin Uwani ya ci gaba da karkawa. Cikin sanyin murya ta ce, "Don Allah ka yi haƙuri Nur." Idon Jafar a lumshe cikin wata irin murya ya furta, "Da aka yi me?" Shiru Uwani ta yi don ba ta da amsa, Jafar ya ci gaba da aika mata zafafan sakwanni tun Uwani na ɗari-ɗari tuna huɗubar Aunty ya sa ta ɗan fara sakin jiki tana mayar masa da martani. Hakan ba ƙaramin hautsina shi ya yi ba, ta saki jiki tana ba shi duk kulawar da ta dace. A lokacin da Uwani ta sakankance suna faranta ran juna, ta tsinkayi Jafar na addu'ar da Annabin rahama ya koyar ga magidanta ya yin tarawa da iyali. Allahumma janibnashshaiɗan, wa janibnashshaiɗanu marazaƙtana. Babu zato ta ji baƙon al'amarin da ba ta taɓa ji ba, duk yadda Uwani ta yi yunƙurin dakatar da Jafar abin ya gagara. Hakan ya sa ta saki kuka cikin jin raɗaɗi da azaba, Jafar bai fahimci halin da take ciki ba har sai ya samu nutusuwa ya dawo hayyacinsa. Ganin yadda Uwani ta yi tuɓus ya sa ya taimaka mata suka gyara kansu, a jikinsa ya kwantar da ita cikin so da ƙauna ya furta. "Allah Ya yi miki albarka!" Fuskar Uwani kumbure idonta cike da ƙwallah ta ce, "Ni dai ba zan sake kwana a nan ba sashen Aunty zan koma." Maganar Uwani ta so ba shi dariya, ya saki murmushi ya ce. "To idan kin je ta ce me ya kawo ki kwana wurinta ki ce mata me?" Shiru Uwani ta yi hawaye na zuba, wuyanta ya ji ya ɗauki ɗumi. Ya ɗauko magani ya ɓallo mata ya ba ta tasha, sannan ya sake rungumo ta jikinsa yana sake ji wani abu na fisgarsa a kanta. Tana nan kwance sai saukar numfashinta ya ji bacci ya yi awon gaba da ita, gyara mata kwanciya ya yi ya ci gaba da yawo da hannunsa a cikin jikinta. Cikin bacci Uwani ta ji Jafar na shirin sake biya mata karatun da ya biya mata da farko, ɗumin hawayenta ya ji na sauka a fuskarsa. Ta saka hannu tana yunƙurin ture shi, cikin wata irin murya ya furta. "Don Allah kada ki dakatar ni." Jafar ya ci gaba da aika mata saƙonnin faratan zuƙatan ma'aurata, tuna nasihar Aunty ya sa ta sake daurewa ta ba wa Jafar haɗin kai har ya sake biyan buƙatarsa. Washegari Uwani da zazzaɓi ta tashi, ga rashin ƙwarin jiki. Don haka Jafar da kansa ya haɗa musu breakfast, Uwani kuwa sai sake shagwaɓe masa take yi kamar yadda Aunty ta koya mata. Shagwaɓarta ba ƙaramin susuta Jafar ta yi ba hakan ya sa wuni guda ya gagara sukuni, sai dai Uwani sai ta yi kamar ta dakatar da shi sai ta tuna nasihar da Aunty ta dinga jera mata. Wuni guda Jafar a tare da Uwani ya ƙare shi, wani abin da Jafar yake yi Uwani har mamaki take yi don ko kaɗan ba ya jin kunyarta. Sosai take mamaki da kunyarsa, don wani abin sai dai shi ya ce ta aiwatar masa da abin da yake muradi game da ita. Rashin gilmawar Jafar ya sa ran mami ba ƙaramin ɓaci ya yi ba. Don haka ta aika Auta kiransa a lokacin an idar da sallar la'asar. Bugun ƙofar da suka ji ne ya sa Jafar ya nufi ƙofar yana faɗin. "Waye?" "Yaya Jafar ni ce." Guntun tsaki ya saki ya zura doguwar rigarsa sannan ya buɗe ƙofar sai dai bai ba wa Autar dama shiga ba saboda yanayin shigar da ke jikin Uwani. "Mami ce take kiranka Ya Jafar." Amsa mata ya yi sannan ta wuce, tura ƙofar Jafar ya yi ya koma wurin Uwani ya zauna a kan doguwar kujerar da take kwance. "Jikin naki da sauƙi ko?" Da yake Uwani ta ji maganar da suka yi da Auta ya sa ta ɗan langwaɓe ta ce. "Wallahi har yanzu da zafi, ga kaina ciwo yake." Kanta ta ɗora a cinyarsa, Jafar ya shafa ɗakalallan saman cikin Uwani a ransa ya raya wani tunani. Murmushi ya saki Uwani na shirin magana suka ji shigowar Mami kamar daga sama, da yake Uwani ta tsorata maƙale Jafar ta yi ta saki ƙara da ƙarfi. Ya rungume ta tsam a jikinsa don shi kansa ba ƙaramin tsorata ya yi da bugun ƙofa haɗe da shigowar Mami ba. Turus Mami ta yi tana bin Uwani da wulaƙantaccan kallo, ganin figigiyar rigar da ke jikinta ko cinya ba ta rufe mata ba. Ta saki dogon tsaki ganin irin ruƙon da Jafar ya yi mata. "To bita zaizai sai ka taso mu je, wato sabida ka saka mace a gabanka na aiko kiranka ka share ko?" Sai a lokacin Jafar ya iya motsawa, ya miƙe da sauri ya ɗan tsaya ta gaban Uwani don ya kare ta. Sam bai ji daɗin abin da Mami ta yi ba, murya a maƙoshi ya ce. "Dama yanzu zan fito Mami." "To wuce mu je." Mami ta furta tana nuna masa hanya. Jafar har ya yi gaba Uwani ta tashi zauna tana faɗin, "Wash Allahna, wallahi Ya Jafar da ciwo." Waigowa ya yi da sauri ya ce. "Bari na dawo sai na karɓo miki magani." Ganin irin rawar jikin da Jafar yake yi da Uwani ya sa Mami ta fahimci mai afkuwa ta gama afkuwa tsakaninsa da Uwani. Saboda haka koda suka fita ta rufe shi da faɗan babu gaira babu dalili. "Ka buɗe kunnenka da kyau ka saurare ni, ba za ka mayar da ni ƙaramar mutum ba. Ina aka kwana a magaar sa ranar aurenku da Safna?" Jafar ya ɗan sosa kai, don sai a lokacin ya tuna rabonsa da waya da ita tun daren jiya. "Maganar tana nan Mami..." "To a yau ka je ka samu mahaifinka ka sanar da shi kana son ya kira mahaifin Safna domin su je a tsayar muku da lokacin aure, wallahi-wallahi Jafar idan ba ka same shi a yau ba sai ranka ya yi mummunan ɓaci. Sakare ina ganin ka mai hankali ashe na banza ne, har za ka zauna yarinya ƙarama tana wasa da hankalinka. Me aka yi, aka yi Uwani? Wacce tsiyar za ka tsinta a jikinta? Tun wuri ka fita daga idona na rufe, idan ba haka ba sai na ɓata maka rai." Jafar shiru ya yi yana jin kalaman mahaifiyarsa na saukar masa tamkar maɗaci, sai da ta yi ta gama sannan ta sallami Jafar ya koma sashensa. Ganin yadda Jafar ya koma a sanyaye ya sa Uwani ta sha jinin jikinta, a wannan karon zuciyarta ta kai wuya da abin da Mami ta yi mata. Sai da ya zauna sannan ta zauna a kusa da shi, idanunta cike da hawaye. "Tun da ƙuruciyata kafin hankali ya ratsa ni na gama tantance so da ƙiyayya na fara fuskantar tsana daga wurin mahaifiyarka, ba tun yau ba na san mahaifiyarka ba ta sona kuma ba ta ƙauna ba. Ya Jafar!" Uwani ta kira shi da wata irin murya, kallonta ya yi ta ci gaba da cewa. "Idan har zamantakewa ta da kai ba za ta haifar da samun ɗa mai ido a tsakaninka da mahaifiyarka ba don girma Allah ka sawaƙe mini. Na sani ka sani a lokacin da aka aurar da mu babu mai son ɗaya daga cikinmu, ni da kai auren haɗi ne. Mahaifiyarka ba ni take muradi ta kasance abokiyar rayuwarka ba, ina ganin zai fi dacewa ka ba ni takarda ta, ka auro Safna idan ya so ni ma zan samu wanda zai so ni kuma mahaifiyarsa ta ƙau..." A hargitse Jafar ya buga mata wata mahaukaciyar tsawar da ta sa ta katse kalaman bakinta. "Kina hauka ne? Ni kike faɗa wa ki je ki auri wani namijin? Na faɗa miki zan iya rayuwa babu ke?" Jin haka ya sa Uwani ta rushe da matsanancin kuka, jikinsa ne ya yi sanyi don haka ya janyota jikinsa don ya san duk kalaman da ta faɗa a kan mahaifiyarsa daidai suke. Amma ta yi wa zuciyarsa adalci idan har ta ce ya rabu da ita? "Duk maganar da za ki faɗa mini ki faɗa amma kada ki sake faɗa mini kalmar rabuwa." Uwani ta ɗago cikin hawaye ta ce. "Amma me ya sa Mami ba ta ƙaunata? Me ya sa duk kyautatawar da zan yi mata ba ta yi mini kallon soyayya sai na tsantsar ƙiyayya? Me ya sa..." "Saboda a faɗin duniya ba kowa ne Allah Ya ƙaddara zai so ka ba, daga ni har ke haka abin yake a gare mu. Don Allah kada ki damu da wannan, halin Mami ba baƙo ba ne a wurinki don haka kada ki ƙara wa kanki ciwon kai." Jafar ya jima yana lallashin Uwani har sai da ya ga ta huce sannan suka ci gaba da hira, a ɓangare ɗaya yana ayyana hanyar da zai bi domin ya sanar da Safna alaƙar da ke tsakaninsa da Uwani. Don a yadda yake jin ta a ransa ba zai iya rabuwa da ita ba, ita ma kuma Safna wata sashe ce a cikin zuciyarsa. Laifin Mami yake gani ƙarara, don da ta bi ta shawarasa da ya ce a sanar da Safna da hakan duk ba ta faru ba. Uwani sai da ta kwana biyu cir ba ta leƙa sashen Aunty ba saboda rashin ƙwarin jiki da irin kulawar da yake ba ta, don gabaɗaya wata irin kunyar Aunty take ji. "'Yata ai tun jiya muke kewarki ni da Auta, na ce Jafar dai ya ɓoye mini ɗiya." Uwani ta sunne kai a kunyace, sai da Auta ta fita daga ɗakin sannan Aunty ta ce. "Ina fatan dai duk huɗubar da na yi miki ba ta tashi a banza ba?" Uwani ta gyaɗa kai tana murmushi. "Ai na ga alama ga shi kwana biyu amarci ya karɓe ki har wani fresh kika yi." Aunty ta faɗa cikin sigar zoyala. "Kai Aunty wallahi kina ba ni kunya." Uwani ta furta. Hira suka sha daga baya Auta ta dawo tana tsokanar Uwani, magriba na ƙaratowa Aunty ta kora Uwani sashenta. Sannu a hankali wata irin shaƙuwa da soyayya mai ƙarfi ta ƙara shiga tsakanin Uwani da Jafar, a yanzu kam sosai Uwani take zagewa tana faranta ran mijinta, wani lokacin har tsokanarta yake ya ce kamar ba ita ke jin kunyarsa a baya ba. Jafar ya samu Daddy da maganar auren Safna, a nan Daddy yake ce masa ya bari a ƙarasa yin fulastar gidansa idan aka yi fenti sai a tsayar da lokacin aure, don ba ya son daga baya a ɗaga saboda sha'nin gini da kashe kuɗi. Lokacin da Jafar ya ga tsarin ginin da Daddy ya yi masa ya ji daɗi sosai, sai dai a ranar da su Mami suka je suka gano gidan kwana ta yi tana yi wa Daddy sababi. Wata irin tsanar Uwani ta sake mamaye ta don gani take ba ƙaramin tozarci ta ja Daddy ya yi mata ba, a ce wai kamar Safna ce za a haɗa ta zama da kishiya. Babban tashin hankalinta ma bai wuce ta wacce hanyar za ta sanar da Hajiyan Safna ba, ga shi Daddy ya ce Uwani ce za ta fara tare wa a gidan kafin a ɗaura aurensa da Safna. Watan Jafar guda da dawowa Uwani ta fara wani irin ciwon kai da zazzaɓi, kasala yawan bacci da tashin zuciya. Hatta abinci idan ta girka shi ba ta iya ci, don haka kusan koyaushe tana can sashen Aunty. Da yake ita ma cikinta ya tsufa sosai Auta ce take hidima da su, a hankali Aunty ta fara fuskantar kamar ciki ne da Uwani amma sai ta bar abin a ranta. Ita kuwa dama Auta tuni ta ranfo jirgin Uwani hakan kuma ba ƙaramin daɗi ya yi mata ba, sai ta yi kamar ta sanar da Mami sai kuma ta fasa don ta san ba za su wanye lafiya a kan maganar ba. Watan Jafar biyu cif da dawowa aka tsayar da ranar aurensa da Safna sati huɗu masu zuwa, kuma a ranar ne Allah Ya sauki Aunty lafiya ta haifo jaririnta ƙato kyakkyawa. Cike da zumuɗi Shukra ta zo gidan a lokacin 'yarta ta yi wayo sosai, Mami gabaɗaya ta tarkata su a gefe don ta ce asirin da Aunty take yi musu ita da Madina ne kaɗai bai kama ba. Kasancewar jinkirin haihuwar da Aunty ta yi ya sa lokaci ɗaya dangi, 'yan uwa da abokan arziƙi aka shiga turuwar zuwa yi mata barka. Uwani ita da Auta kuwa tamkar su haɗiye jaririn. Tun ana saura kwana biyu su Daddy za su je saka ranar aurensa d Safna yake cikin fargaba, damuwarsa ɗaya yadda Uwani za ta karɓi Safna da ita kanta yadda Safna za ta karɓe ta. Dawowarta daga sashen Aunty ta same shi ya yi shiru yana nazari, dama ta fahimci yana cikin damuwa a 'yan kwanakin nan. "Me yake damunka Nur?" "Zauna mu yi magana" Zama ta yi a sanyaye don ta san wata muhimmiyar maganar zai yi mata. "Ɗazu su Daddy sun je an tsayar da ranar aurena da Safna nan da sati huɗu masu zuwa, kuma an kai har da kayan lefe. Ke ma zan tura miki kuɗin da za ki sayi duk abin da kike buƙata, na san Mami ba za ta yarda ta haɗa miki ba shi ya sa ban ba ta ba." Dam ƙirjin Uwani ya buga, wani irin yammmm ta fara ji a saman kanta. Ƙirjinta na bugawa ta fara maimaita sunayen Allah a cikin ranta. "Zan auro Safna ne ba don..." Hannu Uwani ta ɗaga masa fuska babu walwala ta ce. "Daga lokacin da na aure ka ya ci a ce na haddace kalamanka a kwanyata, Safna ita ce zaɓinka, farincikinka kuma abokiyar rayuwarka. Allah Ya sanya alkairi, Ubangiji ya sa tsohuwar gidan ce." Daga haka Uwani ta miƙe ta shige ɗaki, sam bai ji daɗi ba duk da ya san kalaman da yake maimaita mata kenan a baya, amma a yanzu fa? Ya wurga wa kansa tambaya. Ɗakin ya shiga don ya lallashi Uwani sai dai duk yadda ya so ya shawo kanta, ta ƙi ba shi haɗin kai. Tun daga wannan ranar zaman Uwani da Jafar ya sauya, hakan ya sa abin duniya goma da ashirin ya haɗe masa. Duk wani abu da ya kasance haƙƙin Jafar ne za ta sauka masa amma babu wasa ko sakin fuska a tsakaninsu, a haka suka yi ta tafiya har aka yi sunan jaririn Aunty inda ya ci sunan Kamal ana kiransa da Abid kasancwar sunan mahaifin Aunty ne. Lokaci ɗaya Uwani da Jafar suka yi wata irin rama, Aunty da Auta ba su kawo komai a kan Uwani ba sai suka yi tsammanin ko laulayi ne ya saka ta rama. Wane tudu wane gangare Mami ta gano Uwani na da ciki, hakan ya sake ɓata mata rai take jin tamkar ta kama Uwani ta shaƙe ta, ta mutu har lahira. Jafar ganin ya gagara shawo kan Uwani ya sa wata rana da daddare ya nufi sashen Aunty, bayan sun gaisa ne ta ga Jafar ya sunkuyar da kai ƙasa yana son yin magana da ita yana jin nauyi. Fahimtar haka ya sa ta ce. "Jafar ko akwai wani abu ne?" "Am dama Aunty ba wani abu ba ne, don Allah cewa na yi ko za ki tambayi Uwani ko akwai abin da yake damunta, tun dai bayan da na sanar mata maganar auren nan na gagara gane kanta." Aunty ta riƙe baki ta ce. "Ita Uwanin?" Da sauri Jafar ya ɗago ya ce, "Eh amma don Allah Aunty ba faɗa za ki yi mata ba." Murmushi Aunty ta yi tana mamakin yadda Uwani ta tsare gida wai har Jafar yana jin shakkunta. "Tashi ka je Jafar ba zan mata faɗa ba, kasan yaran nan da rashin hankali." Godiya ya yi wa Aunty ya fita, Aunty ta sa Auta ta kira Uwani tana shigowa kuwa ta rufe Uwani da faɗa. A sannan ne ta gane kuskurenta musamman da Aunty ta sauko tana lallashinta tana nuna mata hanyoyin da za ta sake bi ta saye zuciyar mijinta. Ƙamshin tafasowar shinkafa ta ji daga ɓangaren Mami, da sauri Uwani ta toshe hancinta jin amai na yunƙurin taso mata ta ce. "Aunty bari na wuce wallahi warin nan ya fara hautsina mini ciki." Da sauri Uwani ta fita bisa tsautsayi suka yi karo da Mami, kwanon hannunta ya faɗin ƙasa. A zafafe Mami ta ɗauke Uwani da mari, cikin tsana ta furta. "Ke wacce irin dabba ce da ba kya gani kina tafe kanki a sama kamar raƙuma." Dafe kunci Uwani ta yi ido cike da ƙwalla ta ce, "Ban sani ba amma don Allah ki yi haƙuri Mami." Mami ba ta amsa mata ba, Uwani ta dubi Mami da ke tokare da ƙofa ta ce. "Mami zan wuce." Don ji take warin tafasar shinkafar yana ci gaba da bugarta. "Zo ki hankaɗe ni ki wuce." A hankali Uwani ta je za ta gegare ta gefe wani irin amai ya taso mata, kafin ta fita ta fara kyalaya amai har jikin Mami. A ƙazance Mami ke wurga mata mugun kallo takaici na cinta, zafafan mari biyu Mami ta sake sauke mata kafin ta yi magana a ƙufule Uwani ta ce. "Mami wai me na tsare miki ne a rayuwar duniya, bakin gwargwado ina baku girmanki a matsayinki mahaifiyar mijina amma ba kya gani. Kada ki manta fa kema 'ya'ya mata gare ki ba ki san gidan da za su je..." Mami ba ta gama jin maganar Uwani ba ta rufe ta duka cikin ɓacin rai, haushin da take ji na Uwani a tsawon shekaru ne ta sauke mata shi. Cikin azaba Uwani ta fara ƙwallah ƙara jin Mami ta kai mata wani wawan dukan a ƙasan cikinta. Lokaci ɗaya jini ya ɓalle mata, numfashinta ya fara ɗaukewa. Shigowar Daddy, Jafar da Aunty ya yi daidai da ɗaukewar numfashinta. Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan number 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 *DoctorMaryamahGraphics and Data Services.* MTN •1gb ₦300 •2gb ₦600 •3gb ₦900 •5gb ₦1500 AIRTEL 1gb ₦350 •2gb ₦700 •3gb ₦1.050 •5gb ₦1.750 Glo •1gb ₦300 •2gb ₦600 •3gb ₦900 •5gb ₦1500 9mobile 1gb ₦350 •2gb ₦700 •3gb ₦1.050 •5gb ₦1.750 Our Services:- •Data Bundles •Airtime purchase •Cable TV subscriptions •Recharge card •Electricity Bills payment •Converting Airtime to cash •WAEC, NECO and jamb pins Make payment into:- 3195402912 Firstbank Maryam Ibrahim 8136402046 Opay Maryam Ibrahim Send the receipt into:- +234 701 714 8194 Available 16hours📌 from 6am to 10pm. And All types of different Logo invitation card and vide, save the Date and more_____ For more info:- 08136402046 A hargitse Jafar ya yi kan Uwani ya ɗago ta yana jijjigata, yaraf ya ji ta faɗa jikinsa babu numfashi har lokacin jini bai daina bin ƙafarta ba. Kuka Aunty ta fasa cikin tashin hankali ta riƙo hannun Daddy tana faɗin. "Daddy ta kashe ta, Uwani ba ta numfashi." Jikin Daddy har rawa yake yi saboda ɓacin rai. "Jidda! Jidda! Ki tashi don Allah ni ne nake yi miki magana." Jin har lokacin babu numfashi a jikinta ya sa Jafar ya dubi Daddy jikinsa na karkarwa ya ce. "Daddy ba ta jina, Daddy babu numfashi a jikinta." "Ɗauko ta mu wuce asibiti babu lokaci." Abin da Daddy ya iya faɗa kenan ya yi gaba, Jafar ya ɗauki Uwani ya fita da ita a guje kamar zautacce. Auta tana rakuɓe a gefe ban da hawaye babu abin da take yi. "Wallahi ke dai ban san irin baƙar zuciya da baƙin ƙudurinki ba, dubi yadda kika yi wa yarinya saboda kawai wani ƙudurinki na banza. Wallahi ki kuka da kanki domin ke ma 'ya'ya mata gare ki." Aunty ta faɗa cikin ɓacin rai, don ta gama kai wa wuya. Tun da ta zo gidan wannan ne sa'insa na farko da suka taɓa yi da Mami. Daddy ne ya shigo rai a ɓace ya dubi Mami ya ce. "Ki rubuta ki ajiye duk abin da ya samu 'yar mutane, wallahi a kaf faɗin duniyar nan babu mahalukin da ya isa ya hana hukuma ta yi aiki a kanki." Daga haka ya fice daga ɗakin cikin damuwa. Jafar na fita suka yi kiciɓus da Dada ita da Baba Isuhu sun shiga gate ɗin gidan a mashin ɗinsa, kaɗan ya rage Dada ba ta faɗo daga kan mashin ba saboda sauri ta ƙarasa ta ji abin da yake faruwa. Yanayin Uwani kaɗai ta gani ta fashe da kuka tana faɗin, "Kai Jafaru ka faɗa mini abin da ya samu Uwani, wallahi dama haka kawai tun safe nake fama da faɗuwar gaba. Jafaru wai faɗowa ta yi daga bene ko kuwa?" Jafar bai iya tanka wa Dada ba ya saka Uwani a cikin mota, hakan ya sa Dada ta ci gaba da ɓarka kuka hankali a tashe. Jin muryar Dada ya sa Aunty ta ƙarasa gate ɗin, cikin kuka ta ce. "Aunty Saratu ce ta mata duka, Dada matar nan ba ta da imani." Wani irin ɓacin rai ne ya mamaye Dada, a zuciye ta yi ƙwafa sannan ta ce. "Shi kenan tun da har abin ya kai da haka, ido biyu za ta hallaka mini jika. Mamman mu wuce da ita asibiti ni na san abin da zanyi." Daddy ya karɓi key ɗin a hannun Jafar saboda ya lura da yadda yake a kiɗeme ba zai iya driving ba. A kujerar baya Dada ta zauna ta tallafo Uwani da har lokacin ba ta numfashi, ta share hawaye a zuciyarta tana jinjina rashin imanin Mami. Jafar ya shiga gaba sannan Daddy ya fisgi mota ya yi asibitin Hamdala Clinic. "Yanzu Mami abin da kika aika kin kyauta? Mami za ki so a ce Aunty Shukra ake wa abin da kike wa Uwani, Mami kada ki manta ita ma fa 'ya ce kamar mu! Yanzu wa gari ya waya? Me za ki cewa Ya Jafar? Don Allah idan wani abu ya samu Uwani ba fata nake yi ba, ko mutuwa ta yi wa gari ya waya? Ki yi tunani Mami, kada ki bari son zuciyarki ya kai ki ga halaka." Auta na gama faɗa wa Mami haka ta shige ɗakinta tana hawaye. Lokacin da su Jafar suka ƙarasa asibitin da farko ce wa suka yi ba za su karɓi Uwani ba sai dai jami'in ɗan sanda, don haka Jafar ya gabatar da kansa. Da aka nemi statement ɗin abin da ya faru kai tsaye Daddy ya zayyane abin da faru, agajin gaggawa suka fara ba ta haɗe da allurai. Da ƙyar suka samu jinin jikinta ya daina zuba, suka shiga kiciniyar yadda za su samu numfashinta ya daidaita. Sun ɗauki lokaci mai tsawo sannan Dr Humaira ta fito tana sharce gumin fuskarta, da sauri Jafar da Daddy suka tare ta suna jera mata tambaya. Ta kalle su fuska babu walwala ta ce, "Waye mijinta a ciki?" Da sauri Jafar ya amsa, Daddy shi ma ya furta. "Ni mahaifinta ne." Jinjina kai likitar ta yi sannan ta ce. "Ku same ni a office." Gabaɗaya suka amsa mata lokaci ɗaya. "Garin yaya kuka bari haka ta faru da yarinyar nan bayan kunsan tana ɗauke da juna biyu?" Ƙirjin Jafar ya buga, a zabure ya ɗago jin Uwaninsa na ɗauke da juna biyu. Daddy ya dafe kai sannan ya ce. "Wallahi dukkanmu ba mu san hakan za ta faru ba, amma yaya jikin nata yanzu?" Sai da ta zare gilashin idonta sannan ta furta. "Jikinta da sauƙi AlhamduLillah. Amma gaskiya kun yi mugun sakaci, domin ita mai ƙaramin ciki tana buƙatar kulawa." "Amma likita ya ya cikin jikinta?" Jafar ya wurga mata tambaya ƙirjinsa na bugawa. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta ce. "Mun yi mata gwaje-gwaje da hotuna so yanzu akwai result da muke jiran fitowarsa anjima. Idan ya fito ne In shaa Allah za mu san halin da abin cikinta yake ciki, gwaji na farko ya nuna mana Positive daga ba ya kuma ya nuna mana negetive." Wani irin gumi ya shiga karyo wa Jafar, sai da ta gama yi musu bayanan da ya dace sannan suka fice daga ofis ɗin. A harabar asibitin suka hango Aunty a zaune kusa da Dada, Daddy ne ya samu Dada ya kwantar mata da hankali don har lokacin ban da kuka babu abin da Dada take yi. "Maza kira mini Maryama na sanar da ita halin da ake ciki." Dada ta faɗa tana miƙa wa Aunty wayar. "Amma Dada da an bari aga yanayin jikin nata kada a tayar mata da hankali." Daddy ya faɗa. "Idan kuma ta mutu sai mu ce ta zo ta ɗauki gawar 'yarta ko? Mamman ka fita idona na rufe." Dada ta faɗa rai a ɓace. Aunty ce ta kira Maryama tana ɗauka ta miƙa wa Dada, sai da Dada ta share hawaye sannan ta ce mata Uwani babu lafiya suna asibiti. Da yake Maryama mace ce mai kara sai cewa ta yi tun da su suna wurin ita ba sai ta zo ba, jin haka ya sa Dada ta rufe ta da faɗa don haka ta ce gata nan zuwa. Aunty ce ta karɓa ta yi mata kwatancan asibitin sannan suka yi sallama. Cikin ɗakin da Uwani ke kwance Jafar ya shiga, tana kwance tana sauke numfashi sama-sama. Kallon halin da take ciki ya sa Jafar ya ji zuciyarsa na zafi, tabbas uwa-uwa ce amma a wannan karon bai ji daɗin abin da Mami ta yi masa ba. A hankali ta fara motsa hannunta, ya ƙarasa gaban gadon da sauri. Buɗe idonta ta yi tana kallon saman silin ɗin ɗakin, Jafar ne ya matsa ya riƙo mata hannu suna haɗa ido ta ɗauke idonta. Nan take komai ya dawo mata, wata irin tsanar Mami ta ɗarsar mata. "Sannu!" Jafar ya furta a sanyaye. "Ka kai ni wurin Dada!" Dam! Ƙirjin Jafar ya buga. "Me kike so na yi miki?" "Wurin Dada nake son zuwa!" "Dada tana waje!" Ya bata amsa. Fita ya yi yana kiranta, jin Uwani ta farka ya sa farinciki ya mamaye Dada. "Sannu Uwanita!" Jin muryar Dada ya sa Uwani ta fara ƙwalla, ta ɗan runtse ido jin ƙasan mararta da jikinta har lokacin na ɗan yi mata ciwo. "Ki daina kuka kin ji Uwanita, yanzu me kike so?" Uwani ta girgiza wa Dada kai sannan ta ce. "Kawai ki zauna a nan." Da sauri Dada ta amsa mata. Abin duniya goma da ashirin ya haɗe wa Jafar don ya lura Uwani ko kallonsa ba ta son yi, ko sannu ya yi kata ba ta amsawa. Ruwan tea Auta ta kawo aka ba wa Uwani ta sha kaɗan, bayan wani lokaci nurses suka zo suka sake yi mata allurar bacci. Cikin kwana uku jikin Uwani ya yi kyau, kuma duk gwaje-gwaje an yi mata an tabbatar da cikin jikinta na nan bai ɓare ba. Sai dai an gargaɗe su sosai a kan su dinga kula da ita, kuma kada ta dinga aiki kowanne iri har zuwa lokacin da cikinta zai kai wata shida. Tun lokacin da Dada ta ji an sallame su ta ce da Daddy ya wuce da su Kura gabaɗaya, jin haka ya sa gaban Jafar ya faɗi amma sai ya danne don ba shi da bakin magana. Har za su shiga mota Dada ta dubi Jafar ta ce, "Ka kira mini uwarka a yanzu ta same mu a Kura ina son ganinku gabaɗaya." A sanyaye Jafar ya amsa, sannan Dada ta shige cikin mota. Zuwan su Dada gida ya sa gabaɗaya iyalan gidan suka shiga aka ci gaba da sake duba jikin Uwani, sai da duk suka watse sannan Dada ta ja Uwani ɗaki fuska a haɗe ta furta. "Uwani!" Jin yadda Dada ta kira sunanta ya sa Uwani ta fahimci babu wasa a maganarta, Uwani ta amsa sannan Dada ta ci gaba da cewa. "Ki buɗe kunnenki da kyau ki saurare ni, a yau zan zartar da wani hukunci wanda na san ba lallai ya yi miki daɗi ba. Amma ni zan aiwatar da shi ne don na ƙwato miki 'yancinki, domin Saratu ta kai ni magaryar tuƙewa. Ba zan zura ido ta zo ta kashe mini ke a banza da wofi, wallahi idah kika sake kika ba ni kunya sai ranki ya yi mugun ɓaci. Kuma sai ki je ta kashe ki ta kashe banza." Tun da Dada ta fara magana ƙirjin Uwani ya buga, cikin ƙarfin hali ta amsa mata. Gabaɗaya 'ya'yanta sai da ta sa Baba Inusa ya tara mata su, ta sa aka kira mahaifiyar Uwani, Jafar da Uwani suna zaune a gefe kowa da abin da yake saƙa wa a ransa. Sai da Dada ta dube su ɗaya bayan ɗaya ta yi musu sallama fuska a haɗe, don haka suka amsa mata kowa ya sha jinin jikinsa musamman Daddy don ya san wannan zaman ba lallai ya haifar da samun ɗa mai ido ba. "Kamar yadda kuka sani a baya, a wannan wurin da muka zauna a shekarun baya na zartar da umarnin auren Uwani da Jafar. To a yanzu kuma a nan wurin za a warware auren a gabanku." Wani abu ne ya tsarga wa Jafar tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar kansa, lokaci ɗaya ya ji wata irin juya na fisgarsa. "Ba tun yau ba Saratu na san irin ƙiyayyar da kike nuna wa Uwani, to ki sani Jafar ba shi ne autan maza ba wallahi Uwani ba na haufin za ta samu wanda ya fi shi komai a gaba. Duk abin da kika yi mata ki je ke da Allah, amma aure da Jafar har abada Uwani ta gama zama da shi. Yanzu haka saura kwana goma ko takwas ne aurensa da yarinyar da kike so ko? To ya je ya auri zaɓinki, amma ina me tabbatar muku da Jafar zai rubuta wa Uwani takardarta, Allah ya haɗa kowa da rabonsa na alheri." Gabaɗaya ɗakin tsit ya yi kowa ya fara karanta wasiƙar jaki. Dukkansu sun san abin da Mami ta yi sam ba ta kyauta ba amma kuma shi Jafar mene ne laifinsa? "Don Allah Dada ki yi haƙuri..." "Dakata Mamman kada ka faɗa mini maganar banza, saboda ba 'yarka ba ce ko? Tun da kai ka zama sallamamme ba ka isa da gidanka ba Uwani ba za ta zauna matarka ta kashe ta ba, Jafar ko shi kaɗai ya rage a duniya Uwani ba za ta koma gidansa ba." Dada ta furta a zafafe. Baba Inusa shi ma haƙuri ya ba wa Dada gabaɗaya ta rufe su da faɗa, tabbas sun san halin Dada idan ta kafe a kan magana ɗaya babu mai juya ta. Duk yadda suka so shawo kanta lamarin ya gagari Kundila, Jafar ya haɗiyi yawu mai ɗaci zuciyarsa na bugawa ya miƙe zai fita. Dada ta dubi Daddy ta ce, "Idan har na haife ka na isa da kai, wallahi ka sa Jafar ya ba ta takardarta. Idan ba haka ba kuma zan kai shi kotu ya ba ta a can. Kuma umarni ne zan bayar kada na sake ganin ƙafar Jafar a gidan matuƙar ba takardar Uwani ce za ta kawo shi ba, idan har ya kawo mata takardarta to ba zan yi masa iyaka ba.." Jafar bai ƙarasa jin kalaman Dada ba ya fice daga ɗakin rai a ɓace, Daddy ya dubi Mami cikin ɓacin rai ya furta. "Yadda Uwani za ta zauna a gaban Dada kema ki wuce gidan mahaifinki, har sai ranar da Jafar zai ba wa Uwani takardarta zan kawo miki taki. Ki saurare ni da kyau, wallahi kin ji na rantse miki mutuwar auren Uwani daidai yake da naki mutuwar auren." Shi ma Daddy yana gama magana ya fice daga ɗakin, ganin da gaske Daddy yake ya sa Mami ta fashe da kuka sai dai babu wanda ya bi ta da kallon arziƙi. A cikin mota Daddy ya samu Jafar ya kifa kai da sitiyarin mota, murfin motar Daddy ya buɗe yana ambatar sunan Jafar. Yana ɗagowa ya ga hawaye bibbiyu na bin fuskarsa. "Kada ka ga laifin Dada, duk abin da ya faru laifin mahaifiyarka ne. Ka je ka yi addu'a idan zamanka da Uwani ne mafi alheri Allah Ya daidaita ya sanyaya zuciyar Dada, idan kuma babu alheri Allah ya zaɓa muku mafi alheri. Aurenka da Safna saura kwana takwas, idan Allah Ya kaimu aure babu fashi tun da ita ce wacce mahaifiyarka take so." Daddy na gama magana ya saki murfin motar ya wuce tashi motar, kai tsaye gida ya wuce zuciyarsa na suya. Sai da kowa ya watse Uwani ta kwanta a kan gado hawaye na bin gefen fuskarta, tabbas ita kanta a yanzu auren Jafar ta haƙura da shi tun da ta lura mahaifiyarsa rayuwarta take nema ido rufe. A ɓangare ɗaya ta ji wata irin soyayyarsa na nuƙurƙusar zuciyarta. Ta shafa cikinta tuna hirar da suka yi da yake ta zuba mata hirar idan ta samu ciki da irin tarairayar da zai dinga yi mata. Don tun da ta fahimci tana da ciki ta ɓoye masa, ta ci alwashin sai cikinta ya kai wata uku za ta sanar da shi. Koda Jafar ya koma gida falonsu ya wuce, kwanciya ya yi a kan kujera ya zurfafa dogon tunani. Don yadda yake ji ko me za a yi masa ba zai iya rabuwa da Uwani ba, kiran Safna ne ya shigo masa waya a daƙile ya ɗauka murya babu walwala. Jin yanayin muryar Jafar ya sa ta fahimci akwai abin da yake damunsa, tambayar duniya ta yi masa ya ce mata babu komai. Maganar event-event ɗin da za su yi ta yi masa tashin farko Jafar ya ce mata ba zai samu halarta ko ɗaya daga ciki ba, alhalin ba haka suka tsara da shi ba a baya ba. Jin haka ya sa Safna ta rushe da kuka, sannu a hankali ya runtse idonsa yana jin kukanta har cikin ransa. "Ya isa ba na son jin kukan nan!" Jafar ya furta a hankali. "Amma Baby yanzu me kake son ƙawayena su ɗauke ni, wai me yake faruwa na gagara gane kanka ne?" Safna ta yi maganar cike da damuwa, gyara kwanciyarsa ya yi kansa na sara masa ya furta. "Babu komai, yanzu me kike so?" "Zuwanka wurin event!" "Zan zo amma guda ɗaya zan iya zuwa!" "But please..." "Na gama magana please akwai abin da zan yi yanzu." Jafar bai tsaya jin ta bakin Safna ba ya katse wayar. Kashe wayar ya yi gabaɗaya ya miƙe yana kaiwa da kawowa, haka kawai ya ji duniyar ta yi masa zafi. Wani tunani ne ya faɗo masa da sauri ya kunna wayarsa ya lalubo lambar Uwani ya kira, ya yi sa'a kuwa tana shiga amma har ta katse ba a ɗauka ba. Sai da ya kira kusan sau goma sannan Uwani ta ɗauka. Ajiyar zuciya ya sauke a fili sannan ya furta. "Yanzu kin amince Dada ta raba tsakaninmu Hayatee, kin san dai ba zan jure ba. Kin sabar mini da abubuwa kala-kala da ba zan jure rashinsu ba, don Allah kada..." Ƙit ya ji Uwani ta kashe wayar gabaɗaya. Daga can ɓangaren Uwani ta cusa kanta cikin filo ta rushe da matsanancin kuka. Wata irin soyayyar Jafar take ji na ratsa ta har cikin gangar jiki da ruhinta, jin motsin Dada za ta shiga ɗakin ya sa ta yi lamo kamar mai bacci. Mami tana fita kai tsaye gidan mahaifinta ta nufa, ta kira Ibrahim ta sanar da shi abin da Daddy ya yanke a kanta. Har za ta kira Jafar sai kuma ta ji wata irin kunyarsa ta lulluɓe ta, don ba ta san me za ta ce masa ba. Kamar yadda Dada ta sanar da Baba Inusa ana yin sallar magriba ya yi sallama a sashenta, Dada ta dubi Uwani ta furta. "Ga Inusa ya ƙaraso kamar yadda na faɗa miki zai ɗauke mu yanzu za mu kai ki wurin Maryama, wallahi-wallahi Uwani matuƙar na ji labarin kin sanarwa wani wurin da kike sai ranki ya yi mummunan ɓaci. Ɗazu mun gama magana da Maryama za ki koma wurinta da zama har zuwa nan da Allah Ya sauke ki lafiya, daga ni, mahaifiyarki, Inusa sai ke mu kaɗai muka san da tafiyarki. Kuma duk cikinsu babu wanda ban ja kunnensa na gargaɗe shi ba. Duk bayan sati ɗaya ko biyu zan dinga zuwa ganinki In shaa Allah." A sanyaye Uwani ta gyaɗa kai, ta ja akwatinta ta fito da ita a lokacin duhu har ya yi. Babu wanda ya lura da fitar su Dada don haka Baba Yunusa ya ɗauke su zuwa garin da mahaifiyar Uwani ke aure. Tarba ta mutumci aka yi musu lokacin da za su tafi Dada ta ɗauko kuɗi masu kauri ta ba wa Maryama, Aramma da ita Uwanin kanta. Baba Yunusa ya sauke musu kayan abincin da Dada ta saka shi saya, a fili Aramma ya nuna rashin jin daɗin haka. Dada ta ce masa babu komai don ba daɗi a ɗora wa mutum nauyi, musamman da ake fama da yanayin rayuwa. Dada ta ja kunen Aramma sosai, don ta san matuƙar Jafar ya farga Uwani ba ta nan tabbas zai zo nemanta nan gidan. Aramma har ƙofar gida ya raka su yana sake jaddada wa Dada riƙe alƙwarin da ya yi mata. Dada ta koma gida da kamar minti talatin sai ga Jafar ya je gidan afujajan, tana daga zaune ta hango shi a tsaye. Ta ɗan ƙanƙance ido ta ce. "Waye haka a tsaye zai shigo mini ɗaki a tsakar daren nan?" Jafar bai amsa ba ya shiga ɗakin ya zauna a kusa da ita ya ce. "Dada ina matata?" Sheƙeƙe Dada ta kalle shi ta ce, "Yanzu kam Uwani ai ta tashi daga matarka, miƙo mini takardarta." Dada ta yi maganar tana miƙa masa hannu. "Wallahi ba ki isa ki raba ni da matata ba Dada, haka kawai ina son matata tana sona ki ce za ki raba mu. Wallahi ki guji fushin Ubangiji..." Tun Jafar bai gama magana ba Dada ta fashe da kuka, ta janyo wayarta ta yi latse-latsenta ta kira. Ana ɗaga wa ta furta. "Mamman wallahi tun wuri ka ce Jafaru ya fita daga idona." Daga can ɓangaren aka ce. "Dada Abuwa ce ba lambar Daddyn yara kika kira ba sai dai a ba shi wayar." Cikin sauri Dada ta ce. "Maza ba shi kada Jafaru ya rufe ni da duka." Daddy yana karɓar wayar ya ce. "Barka da dare Dada." "Wallahi Mamman idan ba ka yi mini iyaka da Jafaru ba Hukuma za ta raba mu, saboda Allah ya zo ya har tsakar ɗakina ya rufe ni da faɗa. Wai ina matarsa? Yo to ta ina Uwani take a matsayin matarsa? Ni ka gaya masa ma Uwani ba ta garin nan gabaɗaya, kuma gobe-gobe zan sa Isuhu ya kai ni kotu Jafaru ya ba ta takardarta." Hankali a tashe Daddy ya ce. "Dada ina kuma Uwanin ta tafi?" "Wa muke yi wa sallah Mamma?" Da sauri ya ce. "Allah mana Dada. "To wallahi tallahi Uwani ba ta gidan nan, kai ita da sake dawowa ma sai Allah ya sauke ta lafiya. Tsoron matarka nake haka kawai watarana ta biyo dare ta shaƙe ta har lahira." Jafar bai gama jin bayanin Dada ba ya faɗa ɗakinta, wayam ya gani babu Uwani babu alamarta ya shiga bi sashe-sashe na gidan yana tambaya, duk inda ya je sai dai ace masa ba ta nan yawanci ma a bakinsa suke jin Uwani ba ta gidan. Jafar ya dafe kansa a haukace yana jin tamkar zuciyarsa za ta faɗo daga ƙirjinsa. Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank shaidar biya ta wannan no 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Hankali a tashe Jafar ya koma ɗakin Dada don sai a wannan lokacin ya tabbatar da abin da ta faɗa game da rashin Uwani a gidan, yana shirin yi mata magana ya ji ta ce. "A toh wallahi matuƙar Jafaru zai dinga zuwa yana yi mini maganar Uwani na dai faɗa maka sharaɗina, a can uwarsa ta hana yarinya sukuni. Yanzu kuma ta bar gidan ma zai hana ta yin laulayi cikin kwanciyar hankali." Daddy ban da haƙuri babu abin da yake ba wa Dada, sai da ta yi faɗa mai isarta sannan ta miƙa wa Jafar waya. Saboda tsabar takaici ko kallon Dada bai yi ba, ganin ba shi da niyyar karɓar wayar ya sa Dada ta ce. "Kasan dai Saratu ta fika ƙarfin jini Mamman, to ga shi dai ƙiri-ƙiri na yi wa Jafaru magana ya mayar da ni garu, ni dai ka dubi Allah da Annabi Mamman ka ce Jafaru ya fice mini daga ɗaki. Kwarankwatsa dubu ko bai shaƙe ni ba yanzu na san kaɗan ya rage masa." Daddy ne ya katse wayar Dada nan take ya kira ta Jafar, kamar ba zai ɗauka ba ya haɗiyi yawu mai ɗaci sannan ya ɗauka. "Daddy..." "Ka zo gida yanzu ina son ganinka." Iya abin da Daddy ya faɗa kenan ya katse wayarsa. A ƙufule Jafar ya dubi Dada ya ce. "Wallahi Dada idan ba ki kai ni wurin hukuma ba ni zan kai ki, kuma duk abin da ya faru da matata ke ce." "Sai ka fara kai ƙarar Saratu tukunna, kai wallahi bari Inusa ko Isuhu su zo Saratu ma ba ta daki Uwani a banza ba, sai na kai ƙararta idan ya so Jafaru ka ɗaure ni har igiya ta yi saura." Jafar bai tanka mata ba ya fita cikin ɓacin rai. A hanya ya ci karo da Na Madina har ya kusa bangaje shi, da mamaki ya bi Jafar da kallo sannan ya shige wurin Dada. Wani irn mahaukacin gudu Jafar yake yi cikin ɓacin rai kamar zai tashi sama, a haka ya ƙarasa gida lokacin Daddy da iyalansa gabaɗaya suna babban falo a zaune. Kowa ka dubi fuskarsa ɗauke yake da damuwa duk da har lokacin Daddy bai sanar da su hukuncin da ya yanke a kan Mami ba. Jafar na shiga ya nemi wuri ya zauna, Daddy ya dube su ɗaya bayan ɗaya sannan ya ce. "Kowannenku ya san abin da ya faru dangane da mahaifiyarku tsakaninta da Uwani, a don haka ne kuma Dada ta yanke hukuncin sai Jafar ya sawwaƙe mata kuma har a yanzu Dada tana kan bakarta don ba ta huce ba." Da sauri Auta ta ɗago tana kallonsa idanunta suka ciko da ƙwalla don ko kaɗan ba ta ƙaunar rabuwar Uwani da yayanta. A nan ne kuma yake sanar da su hukuncin da shi ma ya yanke a kan Mami. Shiru falon ya ɗauka duka zuciyoyinsu na suya, Aunty ta sauke ajiyar zuciya tana faɗin. "Amma Daddyn yara wannan hukuncin ya yi tsauri da yawa a wurin Aunty Saratu, saboda ka ga..." "Na riga da na yanke hukunci, ba na buƙatar wata doguwar magana." Shiru gabaɗaya suka yi, cikin jin haushi Madina ta dubi Jafar ta ce. "To Ya Jafar ba shi kenan ba, tun da dama ba ka taɓa sanar da Aunty Safna kana da aure ba ai ta zo maka gidan sau..." Kallon da Jafar ya wurga mata ne ya sa ta ja baki ta tsuke. Da mamaki Daddy yake kallon Jafar cikin kallon tuhuma. "Kana nufin ba ka taɓa sanar mata cewar kana da aure ba? Hankalinka ɗaya kuwa Jafar? A haka za ka iya riƙe mata biyu?" Jafar da abin duniya ya gama haɗe masa, kamar zai yi kuka ya ce. "Mami ce ta ba ni umarnin haka." Nan take ya kwashe yadda suka yi da Mami, Daddy ya jinjina kai rai a ɓace ya ce. "Ka ci gaba da bin ra'ayin mahaifiyarka a kan cikin gidanka, sai ka auna a mizani duk lilon da take ɗora ka akai mai inganci ne ko kuwa a lilon keken ɓera ne? Ban hana ka yi wa mahaifiyarka biyayya ba amma ka san irin umarnin da za ta ba ka ka ɗauka, yanzu kuma dabara ta rage wa mai shiga rijiya. Ruwanka ne ka sanar mata kana da aure, ruwanka ne ku ci gaba da tafiya a haka. Amma ina mai tabbata maka da sannu-sannu ba ta hana zuwa sai dai a daɗe ba a je ba, kuma akwai ranar ƙin dillanci." Sai a wannan lokacin nadamar hakan ta lulluɓe Jafar, tabbas shawarwarin Mami kaso casa'in da take ba shi ba masu ɓullewa ba ne. "Daddy maganar Uwani fa?" Jafar ya tambaya gabansa na faɗuwa. "Dada ta hau fa dokin zuciya kuma kai shaida ne ba ta iya fushi ba, sannan ina mai ba ka umarni matuƙar maganar Uwani ce za ta kai ka cikin gidan nan, ban lamunce maka a matsayina na mahaifinka ba. Saboda ni kaina sharaɗi ne da umarnin mahaifiyata ta gindaya mini, kamar yadda na faɗa maka ka je ka ci gaba da addu'a amma yanzu haka matarka ba ta cikin garin nan. Dada ta tabbatar mini da ba ta ma garin gabaɗaya, sai ka je ka ci gaba da shirye-shiryen bikinka." Jafar bai tanka masa ba, ya miƙe yana haɗa hanya. A haka har ya nufi sashensu da yake jin ya zame masa tamkar kuffai. "Duk da Aunty Saratu ba ta kyauta ba amma hukuncin da Dada ta ɗauka a wannan karon ya yi tsauri. Don Allah idan an kwana biyu ku sake ba ta haƙuri Uwani ta dawo ɗakinta." Daddy ya jinjina kai cikin damuwa ya ce. "Zainabu har yanzu ba ki san Dada ba, a soyayyar da Dada ke wa Uwani ba na jin a kwana kusa za ta sauko daga dokin zuciyar da take kai. A sanin da na yi wa Dada idan aka matsanta da maganar wallahi tsaf za ta iya kai Jafar gaban kotu a kan sai ya bada takardarta, addu'ar dai ita ce mafita." Aunty ta furta. "Allah Ya kawo mana ƙarshen wannan al'amarin." Gabaɗaya suka amsa da amin, don hukunci gabaɗaya bai yi musu ba. Daga na wurin Dada har na wurin Daddy. Sannu a hankali Jafar ya aura wa kansa zaman cikin ɗaki, haka yake wuni da kwana cikin damuwa ko abinci ba ya ciki. A ɓangare ɗaya kuma Safna ta gagara gane kansa, matsananciyar damuwar da yake ciki ta haifar masa da wata iriyar rama. Sau tari idan Aunty ta aika masa da abinci sai dai a dawo mata da shi, hakan ya sa watarana ta samu Daddy da zancen ya je ya same shi ya taushe shi ko zai rage wata damuwar. Mami tun da ta koma zaman gidan mahaifinta sam bai mata daɗi ba, duk da ta sa Ibrahim ya saya mata kayan abinci da kayan shayi amma zuciyarta kullun azalzakarta take a kan Daddy na can shi da Aunty suna cikin farinciki. Jafar ma ya kira ta ya tambaye ta abin da take buƙata, ta ce masa Ibrahim ya saya mata komai. Don haka shi kuma ya tura mata kuɗi ya ce ta yi wasu buƙatun da su, da yake a lokacin sun samu albashi. Shukra ma sai daga baya take jin labarin abin da ya faru, hakan ba ƙaramin sosa mata zuciya ya yi ba. A yanzu babban tashin hankalin da Mami take ciki bai wuce idan bikin Jafar da Safna ya zo yadda za ta ji da ƙawayenta ba. "Yanzu sai na ce Daddyn yara ne ya turo ni gidanmu? Kai ba zai yuwu ba." Mami ta raya a ranta. "Ko kuma zan gayyato su wannan gidan? Gaskiya ba mutumcina ba ne na gayyato su gidan nan, tun da gidan ƙasa ne." Haka Mami ta dinga saƙa da warwara, a haka har dabara ta faɗo mata wacce ta san za ta fitar da kanta kunyar cikin ƙawaye tun da ta riga da ta gama raba Invitation. Sosai Daddy ya yi masa faɗa da nasiha hakan ne ya sa Jafar yake ɗan shan ruwan tea safe da yamma, sai dai abin da yake damunsa a kullin ya kira layin Uwani sai dai ya ji shi a kashe. Kamar yadda Jafar ya yi wa Safna alƙawarin halartar taron dinner hakan ce ta kasance, kasancewar familyn mahaifi da mahaifiyar Safna duk mutanen Kano ne, hakan ya sa mahaifinta ya yanke shawarar yin bikinta a gidansa da ke Unguwar Sharaɗa. Jafar da Safna sun yi shigar purple kuma ba ƙaramin kyau suka yi ba, katafaren hall ne da ya amsa sunansa wanda duk mahaifin Safna ne ya yi komai. Jafar ya ɗan saki jiki yana 'yar walwala ganin yadda Safna ta damu da damuwarsa, don tun tana tambayarsa har ta haƙura ta watsar tun da amsar a kullin ɗaya ce sai dai ya ce mata babu komai. Mami ita da ƙawayenta sun yi shiga ta alfarma, kuma da yake tana cike da su Dada babu mutum ɗaya daga ɓangaren Daddy da ta ba wa gate pass. Aunty ma da farko ba ta yi niyyar zuwa ba sai Shukra ce ta ba ta gate pass ta yi ta roƙonta sannan ta amince. An yi taron lafiya an gama lafiya cikin farinciki da ƙayatarwa. Daga nan hall kuma Mami kai tsaye gidan Daddy ta wuce, tana zuwa kai tsaye ta wuce ɗakinsa. A lokacin da ta shiga yana zaune a kan kujerarsa, da mamaki ya bi ta da kallo ko gaisuwar arziki ba ta haɗa su ba Mami ta ce. "Daddyn yara kada ka yi mamakin ganina, na zo ne domin a yi bikin ɗana da ni. Idan aka kawo amarya zan yi tafiyata na bar maka gidanka." Ba ta jira cewarsa ba ta fice fuuu Daddy ya bita da kallo, mamaki ya mamaye shi ganin har lokacin babu nadama a tattare da ita. Duk wani abin da ya danganci abinci da hidimar mutane Daddy ne ya damƙa wa Aunty, don haka Mami ta sake ƙullatar Aunty hatta su Dada babu wani kallon arziƙi da yake haɗa ta da su, su ma kuma daga ɓangarensu babu wanda ya yi gigin zuwa sashenta. Washegari ne ya kama ranar Lahadi kuma a ranar ne dubban al'umma suka shaida ɗaurin auren Jafar da Safana a kan sadaki naira dubu ɗari biyu. Bakin Mami saboda farinciki ya ƙi rufuwa, haka daga ɓangaren Safna ji take tamkar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha. "A duk duniyar nan bayan ni ba na jin akwai wacce za ta so ki sama da Dada, Uwani kada ki yi wa Dada mummunar fahimta domin soyayyar da take yi miki ce ta sa ta ɗauki wannan matakin a kanki. Kada ki sake ki ba ta kunya Uwani matuƙar kika bi abin da Dada ta nusar da ke wallahi ba Jafar ba hatta mahaifiyarsa muna zaune sai ta nemi bikonki. Ke dai ki kwantar da hankalinki kada ki saka wa kanki damuwa kin san dai ba ke kaɗai ba ce, ki kula da kanki har zuwa lokacin da Allah zai sauke ki lafiya." Maryama ta yi wa Uwani nasiha, gyaɗa kai Uwani ta yi idanunta na ciko da ƙwallah. Sau tari mahaifiyarta na zama ta yi ta ɗebe mata kewa, haka daga ɓangaren mutanen gidan babu wani bambamci ko ƙyama da take fuskanta. Da yake Uwani ba ta da wuyar sabo har ta saba da 'ya'yan gidan. Uwani tana yawan tashi sallar dare ta kai wa Allah kukanta. Sai dai a kullin ji take soyayya da kishin Jafar na sake nuƙurƙusarta, musamman da ta kasance ranar Lahadi kuma a ranar ne take da tabbacin an ɗaura wa Jafar aure da Safna. Wani abu mai nauyi ta ji ya danne mata zuciya, ta miƙe ta shiga ɓanɗaki sai da ci kuka ta ƙoshi sannan ta yi wanka ta dawo ɗaki ta kwanta. Tun da gari ya waye mahaifiyarta ta lura da yanayinta, tambayar duniya ta yi mata Uwani ta ƙi gaya mata sai ce mata ta yi cikinta ne yake ɗan yi mata ciwo. Yamma liƙis Jafar ya tura mota aka ɗauko Safna, sai da aka fara kawo ta nan gidan Daddy aka kai ta kowanne ɓangare ta gaida su sannan aka sake fita da ita aka wuce da ita gidanta. Ƙawayen Safna kusan su huɗu ne suka zauna zaman jiran sayan baki, da mamaki sai gani suka yi shi kaɗai ya shiga hannuwansa ɗauke da ledoji. Sam Jafar ba shi da ra'ayin zaman wani sayane baki, don haka ganin babu wata fuska ya sa Safna ta yi musu raɗa a kunne. Sallama suka yi masa kowacce ta ɗauki jakarta ta fita, har sun kusa gate Jafar ya bi su ya ce akwai abokinsa Muhammad zai mayar da su gida. Suna fita ya saka sakata ya dawo ciki. Ɓangaren Safna ba ƙaramin tsaruwa ya yi ba, kuma an narka dukiya daidai gwargwado. Da yake Hajiyan Safna ta san Jafar na da ƙani Ibrahim, ko da 'yan jere suka kai mata rahoton sashe biyu ne a gidan daga ita har Safna sai suka yi tsammanin na Ibrahim ne. Don ba a jima ba da Mami ta taɓa yi mata maganar, shi ma Ibrahim ana shirin kai masa kuɗin aure. Shigar Jafar ɗakin babu jimawa Safna ta yaye mayafin jikinta, ba ƙaramin kyau ta yi masa ba. Ya zauna a bakin gado ya sakar mata murmushi. "Cutie kin yi kyau!" Cike da kissa Safna ta sunkuyar da kai ƙasa tana murmushi. Hira Jafar ya ɗan ja ta da shi sannan ya shiga toilet ya watsa ruwa, bayan ya fito ya yi musu masauki a ƙasan carpet. Da kansa ya riƙo hannun Safna ya zaunar da ita, lokaci ɗaya zamansa da Uwani ya faɗo masa a ranar da ya dawo daga Sudan. Wani abu ya ji ya tsaye masa a rai, ya haɗiyi yawu mai ɗaci. Safna ta yi mamakin ganin yadda Jafar ya ɗauki tsokar nama amma ya lula duniyar tunani. "Baby!" Ta furta tana girgiza ƙafarsa. Murmushi ya sakar mata sannan ya kai mata baki, karɓa ta yi ita ma ta ɗauka ta fara ba shi. Sai da suka ci suka yi ƙat sannan Jafar ya umarce ta da ta ɗauro alwala, duk da zuciyarta na ɗar-ɗar amma wani irin farinciki take ji yana ratsa ta. Bayan sun idar da sallah ya jima yana yi musu addu'a sannan suka shafa. Abubuwa da dama idan Jafar ya aiwatar wa Safna rayuwarsa da Uwani ce take faɗo masa, hakan ne ya sa ko a lokacin da yake tarawa da Safna cikin suɓutar ba ki yake ambatar sunan Uwani. Ba ƙaramin kaɗuwa Safna ta yi ba jin Jafar na ambatar sunan wata mace ba ita ba. "Jafar ko yana neman mata ne ban sani ba? Kai ko kaɗan mu'amalarsa ba ta yi kama da ta masu neman mata ba." Safna ta raya a ranta. "Ko kuma dai na yi masa magana?" Ta sake tambayar kanta. Tana cikin wannan nazarin Jafar ya riƙo hannunta ya taimaka mata ta gyara jikinta. Tana son tambayarsa amma a zuciyarta na wasu-wasi, don haka ta rabu da shi ta fara narkewa tana shagwaɓe masa. Bakin ƙoƙarinsa Jafar ya ba wa Safna kulawa sai dai sam ba haka ta yi tsammani daga gare shi ba, a yadda suka zuba soyayya ta yi tsammanin zai nuna mata kulawa fiye da haka. Ko da Jafar bai faɗa mata ba ta san tabbas yana cikin damuwa, domin wani lokacin tsakar dare za ta farka ta ga ya zuba uban tagumi. Amma idan ta tambaye shi wani lokacin sai dai ya ce mata aiki ne ya yi masa yawa, ko ya ce mata wani case ne yake caza masa kai. Auta ta yi zaryar wurin Dada babu adadi a kan ta sanar mata wurin da Uwani take amma fir ta ƙi, babu yadda Auta ta iya haka ta haƙura amma kullin tunaninta bai wuce ina Uwani take ba. Gabaɗaya gidan suke jin sa wani iri daga ita har Aunty don idan suka zauna ba su da aiki sai na jajen Uwani, wani lokacin Auta ta sako maganar Mami don ta kan yi kewar mahaifiyarta. Hakan ya sa wani lokacin Aunty ke samun Daddy da maganar don Auta da Madina ba ƙaramin tausayi suke ba ta ba, a kullin Aunty ta je masa da maganar ba ya taɓa ba ta haɗin kai. Ganin zuru ɗin da Jafar ya yi ba zai kai shi ba ya sa ya fara bibiyar 'yan uwan mahaifinsa, sai dai duk wurin da ya je a kan maganar Uwani amsa ɗaya yake samu, kuma ya yi zaryar gidan mahaifiyarta nan ma an ce masa ba ta nan. Don haka abin duniya ya sake haɗe masa, tun Safna na fushi ta shiga damuwa har ta haƙura ta watsar da komai, tun da ta yi bakin ƙoƙarinta wurin ganin ta gano abin da yake damunsa ta gagara. Kamar yadda Dada ta faɗa kusan duk sati sai ta kai wa Uwani ziyara, ganin zirga-zirgar ta yi yawa ya sa Maryama ta ce Dada ta dinga haƙura har sai bayan sati bibbiyu, da ƙyar Dada ta amince da haka. Uwani ta murje ta yi wani irin haske da yake a yanzu laulayin ya yi mata sauƙi. A kullin ta zauna ba ta da aiki sai kallon hotuna da videos ɗin su ita da Jafar, wani lokacin da ta ci kuka wani lokacin kuma idan ta ga wani video ta yi ta sakin murmushi. Gajiya ta yi da zama babu waya don haka ta sa aka sayo mata wani sabon layi, ta kunna wayarta, tsohon layinta ta ɗora ta lalubo lambar Jafar ta ƙura mata ido. Hawaye ke bin idonta kamar almara sai gani ta yi kiransa ya shigo wayarta, sai da ta yanke aka sake kira hannunta na rawa ta ɗaga wayar ta kara a kunne. Ajiyar zuciyarsa ta ji a fili baki na rawa ya ce. "Bakin tsiwata!" Shiru ta yi tana jin yadda ƙirjinta ke dakan lugude, wani abu ta ji na zagaye ta hawaye ya ci gaba da bin kumatunta. "Don Allah ki yi mini magana ko zan ji sanyi a raina, so da ƙaunarki za su zautar da ni..." Ƙit ya ji ta katse wayar, jikinta har karkarwa yake ta zare layin ta ɗora sabon layinta a kai. Ta jima tana hawaye sannan ta kwanta ta lula duniyar tunani. Abin duniya goma da ashirin ne ya mamaye Mami, don a yanzu babu damar ta ajiye kuɗi ko wani abin da ta zagaya banɗaki ko ta matsa daga wurin za ta neme shi ta rasa, ga shi zaman gidan gabaɗaya ya gundure ta. Duk taurin zuciya da kafiya irin ta Mami ƙuncin zaman da take yi ya sa ta yanke shawar kiran Daddy ta ba shi haƙuri. Sai da ta yi wa Daddy kira ya fi hamsin amma babu ɗaya da ya ɗauka, wayar matar babanta ta ara ta kira shi babu jimawa ta ji ya ɗauka. "Daddyn yara yanzu wayata ce ba za ka ɗauka..." Ba ta gama magana ba ta ji Daddy ya kashe wayar gabaɗaya. A ranar saboda takaici Mami har da ƙwallarta. Kamar Auta na da masaniya haka kawai watarana da ta wayi gari ta ce za je wurin Mami, wuni guda ta yi a wurinta amma a mafi yawan hirar tasu Mami ce ke kawo mata ƙorafe-ƙorafen zaman gidan da take yi. Ko kaɗan Auta ba ta ji daɗi ba, hakan ya sa ta fara nusar da ita illar abin da ta dinga aikatawa a baya. An yin sallar la'asar Auta ta yi mata sallama, haka kawai zuciya ta raya mata ta ƙarasa ta gaida mahaifiyar Uwani. Don tun bayan abin da ya faru ba ta sake ganinta ba. Saɓanin lokacin da Uwani na nan ba sa wata ba su je ba. Sai da ta saya wa Maryama kilin da omo a wani shago sannan ta shiga cikin gidan baki ɗauke da sallama, Uwani na zaune a kan tabarma tana cin wainar fulawa a lokacin cikinta kusan watansa bakwai. Turus Auta ta yi tana kallon Uwani da ta saki baki tana kallon Auta da mamaki. "Uwani dama kina nan?" Auta ta furta a ruɗe. Da gudu Uwani ta tafi ta maƙale Auta ta ce, "Auta ya aka yi kika san ina nan?" Auta ta wurga mata harara ta ce. "Malama ki bi a sannu kada ki yi mini asarar yaro ko yarinya." "Ke fa 'yar iska ce, yanzu dai mu shiga ciki." Uwani ta faɗa ta kama hannun Auta suka shiga ɗakin mahaifiyarta. Littafin kuɗi ne 500 ta acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan no 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Tun kafin su shiga cikin ɗakin Auta take bin Uwani da kallo ganin da ta yi wani irin kyau da wata 'yar ƙiba. "Zo faɗa mini wai me Inna take ba ki kike ci ne? Haka kika haye kika bar mini ɗan uwa yana fama da tunaninki?" Uwani ta wurga mata hararar wasa ta ce. "Ba na son sharri wai mike kika ga na yi?" Auta ta riƙe haɓa da mamaki ta ce, "Yo ai ko makaho ya shafa ki ya san kin yi ƙiba." Ruwa Maryama ta kawo wa Auta tana tambayarta su Daddy sai da suka gama gaisawa ta fita ta ba su wuri. "Uwani ni laifin me na yi da ko a waya ba ki neme ni kin faɗa mini wurin da kike ba? Ko laifin Mami ne ya shafe ni? Wallahi duk yadda muka yi da Dada ta ƙi sanar da mu wurin da kike, yanzu ma rabon zan ganki ne na ce bari na biyo na gaida Inna." Nan take Uwani ta kwashe yadda suka yi da Dada ta faɗa wa Auta, sannan ta ɗora da cewa. "Don Allah kada ki sanar da kowa ga wurin da nake kin san Dada gani za ta yi kamar ni ce na sanar da ku." "Amma haka zan bar Ya Jafar kullin yana yawo kamar zautacce, Uwani kin san halin da ya shiga kuwa?" Gaban Uwani ya faɗi, a sanyaye ta furta. "Ni dai kin ji abin da na faɗa, idan kuma kika janyo mini matsala ai shi kenan." Jim Auta ta yi sannan ta ce. "Babu damuwa, Allah Ya tabatar mana da abin da ya fi alheri. Amma gaskiya zan sanar da Aunty halin da ake ciki, sai dai ita ma zan kwaɓe ta, ko Daddy kada ta sanarwa. Kin san daga baya idan ta ji na san wurin da kike ba za ta ji daɗi ba." Auta da Uwani hira suka sha ta yaushe gamo, Auta ta karɓi sabuwar lambar Uwani. Sannan suka shiga hirar bikinta, don a lokacin bikinta saura wata biyu cif.Sai da aka yi sallar magriba sannan Auta ta yi musu sallama ta tafi, don lokacin ma sai da Maryama ta yi mata magana ganin dare ya fara yi saboda yanayin hanya, Auta ji ta yi tamkar ta kwana don dai babu hali ne. Sai da ta tafi tana hanya ta duba wayarta misscall ɗin Aunty ta gani rututu, gabanta ne ya faɗi ta yi saurin kiran wayarta Aunty na ɗauka ta rufe ta da faɗa. "Auta ina kika shiga ne dare ya fara yi fa, so kike sai Daddynku ya zo ya fara faɗa ko?" Da yake a lokacin Auta ta kusa shiga layinsu a gaggauce ta ce. "Aunty gani ina kusa da gida." Auta na isa gida ta samu Aunty a falo fuska babu walwala. "Hajiya Aunty sannu da gida!" "Wallahi da Daddynku da ya dawo ya yi mini faɗa hukuncinki karɓar wayar hannunki, kuma ki wuce ga tuwo can sai ki kwashe ni na gama aikina." Auta ta ƙunshe dariyarta ganin yadda Aunty ta fututtuke tana faɗa. "To Hajiya Aunty yanzu dai ba na dawo ba, kuma wallahi da wani albishir nake tafe. Amma ni ma sai na ja ajina." Aunty na jin haka ta saki murmushi ta ce. "Zo Autar daddy mana." Auta ta yi ɗakinta tana faɗin, "A'a Hajiya Aunty ni ma yanzu kaya zan cire na kwashe tuwo." Murmushi Aunty ta yi ta wuce ɗakinta. Da daddare bayan sun gama cin abinci Aunty ta dubi Auta ta ce, "Auta ba na son iskanci na lura tun da kika dawo bakinki akwai magana, wai wanne albishir ne?" Sai da Auta ta tashi ta saka sakata a ƙofa sannan ta koma ta zauna murya can ƙasa ta ce, "Aunty don girman Allah ki yi mini alƙawarin idan na faɗa miki babu wanda za ki faɗawa, ciki kuwa har da Daddy." Jim Aunty ta yi tana mamaki ta ce. "Shi kenan na yi miki." "Yau dai ƙafa da ƙafa na je na gano 'yarki Uwani, kin ga yadda ta sauya kuwa?" A zabure Aunty ta ce. "Ke Auta da gaske?" Auta ta saki dariya sannan ta kwashe duk yadda suka yi da Uwani, sosai Aunty ta ji daɗin labarin kuma ta sake alƙawarin ba za ta sanar da kowa ba. Haka ta ce za ta saka lokaci ta je ta gano ta, har lambar Uwani ta ba wa Aunty suka ci gaba da tattaunawa dangane da Uwani. Uwani tana zaune ta ga baƙuwar lamba ta shigo mata, a hankali ta ɗauka sannan ta yi shiru. Daga can ɓangaren ta ji muryar Aunty na faɗin, "Wai dama 'ya za ta guji uwarta ban sani ba." Jin muryar Aunty ya sa Uwani ta saki ihun farinciki tana faɗin. "Sai Hajiya Aunty da kanta." "Ke kunna data na kira ki video call 'yata ta ce mini jikata ta mayar mini da ke uwar mata." Aunty ta furta tana katse kiran. Nan take Uwani ta kunna data, babu jimawa kiran Aunty ya shigo mata. Ba ƙaramin mamaki Aunty ta yi ba ganin yadda Uwani ta yi ƙiba kamar ba ita ba. "Yata wai dama za ki yi ƙiba?" A kunyace Uwani ta saki murmushi. "Zan tambayi Dadynku fita In shaa Allah next week za ki ganmu." Uwani ta amsa sannan ta ce. "Aunty Ina Abid na san yanzu ya manta ni ko" Aunty ta haska wurin Abid da ke bacci ta ce. "Kin gan shi can kayan rigima bacci yake." Cikin wata irin kewarsu ta ce. "Na yi kewarku sosai Aunty." Daga haka sai Uwani ta fara ƙwalla. "Idan kuka za ki dinga yi mini ba zan sake kiranki ba, so kike ki sa kanki a damuwa kina fama da kanki ne?" Uwani ta goge hawayenta tana girgiza kai. Sun jima suna hira sannan ta miƙa wa Innarta bayan sun gaisa suka yi sallama. "Maryama yanzu haka za a ci gaba da azabtar da mijin yarinyar nan kenan? Don Allah ki samu Dada ki ba ta haƙuri a kan zaman yarinyar nan ko yaron nan ya samu sukuni." Aramma ya furta cike da damuwa. "Wani abu ya faru ne malam? Ko zaman Uwani ne ka fara gajiya da shi?" Ajiyar zucuya Aramma ya sauke sannan ya ce. "Wallahi mijin yarinyar nan kusan zuwansa shida kenan ƙofar gidan, kuma duk zuwan da zai yi sai dai na ƙirƙiri wani uzurin na faɗa masa. Ko na ce kin yi tafiya, ko kuma na ce kin je unguwa. Zancensa ɗaya ina Uwani take. Kwanaki sai da ya kai har sha biyun dare a ƙofar gidan nan yana zaman jiranki, da yake ranar na ce kun je garin su Indo. Ni ina ganin da za a roƙi Dada ya ci a ce ta sauko yanzu." Har a cikin zuciyarta tana son zaman Jafar da Uwani domin yana da hankali da nutsuwa, Maryama ta dubi Aramma ta ce. "Malam ba a nan gizo yake saƙar ba, idan ba ka manta ba matsalar ba daga wurin Jafar ba ce. A wannan karon Dada na yin yaƙi ne da Saratu, wallahi na tabbata Dada ba za ta yi abin da zai cutar da Uwani ba. Yadda ta kawo mana ita take ci gaba da ba ta kulawa, mu kawo ido mu zuba mata. Duk wannan abin da yake faruwa watarana sai labari." Jinjina kai Aramma ya yi, a ransa yana tausayin yanayin da yake ganin Jafar. "Mommy akwai fa matsala, wallahi tun da muka yi aure na rasa gane kan Jafar. Na fahimci yana cikin damuwa kuma na lura akwai abin da yake ɓoye mini. Na farko tun da muka yi aure ko sau ɗaya bai taɓa kai ni familynsa daga na Daddy har na Mami ba, kullun magana ɗaya yake mini ba shi time sai weekend. And kowanne weekend ya zo akwai uzurin da yake ba ni, Mommy ni fa ina zargin akwai budurwar da ta ɗauke hankalinsa because wani lokacin ko a cikin bacci haka za ki yana cewa Jidda" Safna ta ƙarasa maganar hawaye na zuba. Daga can ɓangaren Mommy ta ce. "Ki daina zubar da hawayenki a banza kin san dai mu ba irin zama da kishiya ba ne. Mahaifiyata har ta koma ga Allah ba a yi mata kishiya, ni ma kuma ga ni da Daddynki har tsufa ya zo. Sai ke ƙanƙanuwarki za a yi wa kishiya? Ƙyale shi zan kira mahaifiyarsa na ji abin da yake faruwa, yanzu za ki ga aiki da cikawa. Kin san Hajiya Saratu da kuɗi, yanzu zan jefe ta 'yar dubu ɗari biyu. Ina me tabbatar miki har haƙuri sai ya ba ki." Farinciki fal fuskar Safna suka yi sallama. A ranar da Jafar ya koma daga wurin aiki kallon sama-sama ta yi masa saboda yadda Mommy take nuna mata za su saye mahaifiyarsa, shi ma bai bi ta kanta da don abinci ma gabaɗaya cokali bai fi biyar ya ci ba. Dama kuma idan da sabo ta saba da haka, damuwa ce ta mamaye shi da tunanin Uwani da halin da take ciki musamman da a 'yan kwanakin nan yake yawan mafarkinta. Mami na zaune ta ga alert ɗin dubu ɗari biyu daga akawunt ɗin Hajiyan Safna, jiki na rawa ta tafi lalubo lambarta sai ga kiranta ya shigo mata. "Hajiya da kanki haka ai da kin bari na kira." Mami ta furta murya na rawa. "Kai haba Hajiya Saratu ai an zama ɗaya, ya gida ya yara?" Mami ta wayance ta amsa don babu wanda ta taɓa nuna wa ba ta gidan Daddy, hatta Hajiya Falmata duk yadda suke ba ta taɓa sanar da ita ba. Sai da suka gama gaisawa sannan Hajiyan Safna ta fara wassafo ƙorafin Safna, lokaci ɗaya Mami ta fututtuke tana nuna laifin Jafar. Sannan ta ɗora da cewar. "Allah na tuba ma wane maganar budurwa ko zancen ƙarin aure? Jafar ɗin nawa yake kuma duka yaushe suka yi aure? Ban da ma auren zamani ya ci a ce har an fara samun saɓani ne? Amma ki bar ni zai zo ya same ni Hajiya." Mami ta furta sannnan suka yi sallama, har Hajiyan Safna ta kashe Mami ba ta daina bambaɗanci ba. "Wallahi Saratu kin saka kanki a wahala, kwaɗayi dai mabuɗin wahala ne. Ke yanzu a ƙaramar ƙwaƙwalwarki kina ganin wannan ɗan abin da matar nan take ba ki ya fi mutumcinki? A tunaninki har abada ba za ta fasu cewar Jafar na da wata matar har da ciki ba? Yanzu idan watarana suka tabbatar da matar yaron nan har da ɗanta ko 'yarta me za ki ce wa mahaifiyar yariyar nan da ita yarinyar?" Matar mahaifinta ta furta cike da takaici. Cikin halin ko inkula Mami ta ce, "Kafin lokacin zan daidaita komai, ni yanzu ma can gidan Daddyn yara zan je na ba shi haƙuri don na gaji da zaman kaɗaici 'ya'yana suna can wata ƙatuwa na mora." Inna ta saki shewa haɗe da buga cinya ta ce. "Ai Saratu kin daɗe da yin sake, wallahi kin yi sake ɗan zaki ya girma amma za ki ce na faɗa miki, ke dai a juri zuwa rafi watarana tulun zai fashe." Suna gama magana Mami ta kira Jafar ta dinga yi masa faɗa a kan abin da Hajiyan Safna ta faɗa mata, Jafar shiru ya yi yana sauraronta sai da ta gama faɗan sannan ya ba ta haƙuri suka yi sallama. Wata galleliyar atamfa Mami ta saka hannu da ƙafa sun sha ƙunshi gwanin birgewa, sai da ta rangaɗa ɗaurin ɗankwalinta sannan ta nufi gidan Daddy. Ta yi sa'a ta same shi yana zaune a baranda, da murmushi ta ƙarasa wurinsa tana faɗin. "Ranka shi daɗe hutawa ake?" Kallonta ya yi lokaci ɗaya ya ga duk ta lalace, ta ɗan yi duhu ga ramar da ta yi. "Me ke tafe da ke?" Russunawa ƙasa Mami ta yi ta fara jera masa ban haƙuri, sai da ya gama sauraronta sanna ya ce. "Saratu ai ba ni za ki ba wa haƙuri ba, ki je ki samu Dada idan har ta huce a kan Uwani za ta koma ɗakinta fani'ima, ko yanzu Uwani ta dawo za ki dawo ɗakinki. Ai maganar mai sauƙi ce, akasin haka kuma kin ga shi kenan dama kowa ya sayi rariya ai ya san za ta zubar da ruwa." Aunty ce ta ƙarasa wurin hannunta ɗauke da jug ta dire a gaban Daddy, ganin Mami ya sa ta ɗan faɗaɗa fara'arta tana faɗin. "Aunty Saratu ina kwana." Sai da Mami ta goge ƙwallar idonta sannan ta amsa. "Lafiya ƙalau Zainabu ya kwanan yaran?" Aunty ta amsa sannan ta fara ƙoƙarin barin wurin. Da sauri Mami ta tare ta tana faɗin. "Don Allah Abuwa ki taya ni ba wa Daddyn yara haƙuri." Jikin Aunty ba ƙaramin sanyi ya yi ba ganin mace mai isa da izza kamar Mami, tana zubar da ƙwalla har tana roƙonta a kan ta ba wa Daddyn yara haƙuri. Aunty na shirin magana Auta ta nufo wurin hannunta ɗauke da Abid yana kuka, turus ta yi ganin Mami a tsugunne tana hawaye. Ganin haka ya sanyaya mata jiki, ta ƙarasa wurin tana faɗin. "Mami yaushe kika zo?" Mami ba ta iya amsa mata ba sai ƙwalla da ke zubo mata. Har cikin zuciyarsa Daddy bai ji daɗin yanayin da ta riske su ba. Don haka ya dubi Mami ya ce. "Ki wuce gida an jima zan je na samu Dada za mu yi magana." Hakan ne ya ɗan ƙarfafa gwiwar Mami ta miƙe ta yi wa su Aunty Sallama ta fice daga gidan. Fuska a haɗe Jafar ya koma gida ganin haka ya sa Safna ta ɗan sha jinin jikinta, da yake Jafar a ƙule yake da abin da Safna ta yi masa ko kallon kirki bai yi mata ba. Can kan table Jafar ya fara duba wa bai ga komai ba, fuska a haɗe ya furta. "Ina abinci?" "Ban dafa ba!" "Saboda me?" A watse Safna ta ce, "Saboda haka na yi ra'ayi, ni fa gaskiya na gaji wallahi ba zan juri girki kullin ba, saboda ba cin na kirki kake ba." Jafar bai tanka mata ba ya faɗa banɗaki, Safna ta jima tana fakon Jafar a kan wayarsa. Don haka tana ganin ya shiga toilet da sauri ta ɗauki wayarsa ta fara duba whatsapp chats, babu wata baƙuwar lamba da ta gani wacce ta danganci hirar soyayya. Cikin gallery ta duba nan ma babu wasu baƙin hotuna da ba ta san da su ba. Wata folder ta gani an rubuta J&J kamar yadda a folder da ke ɗauke da hotunanta ita da Jafar ya rubuta J&S, ƙirjinta ne ya buga da ƙarfi. Da sauri ta saka hannu za ta buɗe sai gani ta yi akwai key a ciki. Motsin Jafar ta ji zuciyarta na suya ta kafe ƙofar da kallo. "Wannan folder mene ne a cikinta? Kuma mene ne ma'anar sunan da ka rubuta?" Jafar bai tanka mata ba, ya karɓi wayarsa ya juya zai yi gaba. Da sauri Safna ya sha gabansa cikin tsiwa ta ce. "Magana nake yi ka mayar da ni mahaukaciya, wace ce wacce kake soyayya da ita ban sani ba." Jafar ya lumshe ido jin wani abu na sake fusgarsa a kan Uwani, ya watsa mata idanunsa a lumshe sannan ya ɗora hannunsa a gefen ƙirjinsa ya furta. "Wata mai muhimmanci ce a gare ni, ba iya mai muhimmanci ba a duk sauka da hauhawar numfashina na fita da tsantsar so da ƙaunarta..." Tun bai rufe baki ba Safna ta shaƙe masa wuya tana zunduma ashar sannan ta ce. "Wallahi ka yi ƙarya ka tozarta ni Jafar, wallahi ba ka isa. Uban wa ya ce ka fara soyayya da ita..." Jafar hannu ya ɗaga kamar zai mare ta sai kuma ya sauke, ya fisge jikinsa haɗe da hankaɗa ta sannan ya koma falo zuciyarsa na suya. "Wato damar da Safna ta samu a wurin Mami har ta kai haka kenan? Tabbas ya zama wajibi na ɗauki mataki a kanta." Jafar ya raya a ransa. Kuma tun daga wannan ranar ya koma kwanan falo ita ma Safna ta shiga fushi da shi, abin duniya ya haɗe mata. Sai ta yi kamar ta kira Mommynta sai kuma ta fasa, amma hukuncin da Jafar ya ɗauka a kanta ba ƙaramin zafi ya yi mata ba. Dalilin da ya sa suka ci gaba da zaman doya da manja, ganin ba za ta iya jura ba ya sa watarana Safna ta je ta samu Jafar ta ba shi haƙuri don Safna ba ƙaramar soyayya take yi wa Jafar ba. Ta kuma ci burin gano ko wace ce ke ƙoƙarin kwace mata miji, ta ci alwashin ko 'yar gidan uban waye sai ta nuna mata iyakarta. A haka dai rayuwa ta ci gaba da tafiya har lokacin bikin Auta ya ƙarato, duk wani shirye-shiryen biki ita da Uwani suke tsarawa sai Aunty. Wani abin kuma ta kira Shukra a waya su tattauna don Shukra ta sauko sosai ba kamar da ba, kamar wancan karon duk wani abu da ya danganci cimar taro ta cikin gida Daddy ya damƙa wa Aunty komai. Game da kayan kitchen da kayan ɗaki ne Daddy ya kira Mami suka tattauna domin ya ba ta haƙƙinta, saboda kawo wannan lokacin Mami ta haƙura da jiran gawon shanu ta fawwala wa Allah lamuranta. Aunty ta yi rawar gani wurin tsayawa tsayin daka ta gyara Auta tamkar yadda ta haɗa wa Uwani haɗin kayan gyara a wurin BOJUWA 08032773332, hakan ya sake ɗaga darajarta a wurin su Shukra da Daddy. Hatta Mami ta fara zubar da makamanta don ta lura ita take kiɗa kuma take rawarta. "Dada gaskiya babu abin da zai hana ni zuwa bikin Auta, ni fa wallahi zaman gidan ma ya ishe ni a ce kullin ina gida daga asibiti sai gida." Uwani ta furta wa Dada a shagwaɓe lokacin da ta kawo mata ziyara. "Ƙaniyarki Uwani, wa yace miki mai tsohon ciki tana shiga cikin taro? A hir ɗinki ki kiyaye ni, ke ba ki san ana haɗuwa da tanɗau da lasau ba?" Uwani ta tura baki gaba ta ce. "Ai wallahi ni dai kurwata ta fi ƙarfinsu, a wannnan karon sai dai ku yi haƙuri. Don ni fa na gama shirye-shiryen biki hatta jaka da takalmi babu abin ban tanadi na fitar biki ba." Dada ta riƙe baki ta ce. "To ai shi kenan, idan ba ki yi gaddama ba ai ba a ce ke jinin Umaru ba ce." Daga haka suka ci gaba da hira. Da Dada za ta tafi kuwa Uwani ta maƙale a kan dole sai ta bi ta sun tafi tun da bikin Auta saura bai fi kwana huɗu ba. Babu yadda Dada ta iya haka Uwani ta cika akwatinta da komai da ta san za ta buƙata suka wuce da Dada. Tun suna hanya Uwani ta tura wa Auta da Aunty saƙon ta bi Dada, Auta ta ce mata washegari za ta zo daga nan sai su wuce gidan lalle. Cikin Uwani ya tsufa sosai don ta shiga wata na tara, ta yi ƙiba kamar ba ita ba. Ranar alhamis aka fara bikin Auta kuma a ranar ne ta yi bridal shower, ranar Juma'a ya kasance kamu. Duk wani gyaran kai da lalle da aka yi wa Auta tare aka yi wa Uwani, hatta kwalliya a wuri ɗaya aka yi musu. Daga wurin make up ne kuma suka wuce hall ɗin da za a yi kamu. Hall ɗin ya ƙayatu sosai da adon kayan gargajiya, Uwani atamfa lace ta saka wacce aka buga mata aiki a gaban rigarta. Sai ɗaurin ɗankwalin da aka kafa mata ba ƙaramin kyau ta yi ba, musamman da ta yi ƙiba ga cikin jikinta ba ƙaramin karɓarta ya yi ba. 'Yan uwa da ƙawayensu na makaranta sai tsiya ake yi wa Uwani. Tana nan zaune a kan kujera, ita da wasu classmate ɗinsu na makaranta suna hira Safna ta ƙarasa cikin doguwar rigar wani tsadaddan material. A gefen kujerar Uwani ta zauna ta ɗan saki murmushi tana faɗin. "Sannu!" Ɗago kan da Uwani ta yi karaf suka sauka a kanta. Tabbas ko a cikin mafarki ba za ta gagara manta fuskarta ba, duk da ta kwana biyu da ganinta amma kamaninta na nan daram a ƙwayar idonta. Sai ɗan haske da murjewar fata da ta sake yi, ko babu tantama ta tabbata wannan Safna ce. Tunanin Uwani ya katse a daidai lokacin da ta riski muryar Madina tana faɗin. "Aunty Safna ga wurin zama can ko har kin zauna..." Maganar Madina ta maƙale sakamakon ido biyu da suka yi da Uwani. "Na riga na zauna Madina, ba na son ƙarar speaker can." Safna ta furta ta sakin murmushi. Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan no 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 A wayance Madina ta amsa tana barin wurin, cikin zuciyarta tana mamakin irin kyau da murjewar da Uwani ta ƙara yi. Wani abu ne yake taso wa Uwani a zuciyarta, a hankali ta runtse idonta tana karanto duk wata addu'a da tasan za ta sanyaya mata zafin da take ji a cikin ranta. "Mai shanu ya dai? Kada ki haife mana ɗa a filin nan fa, idan abar ta zo wuce mu shiga ɗakin ajiyar gift kin san tsaf zan karɓi haihuwarki." Ɗaya daga cikin ƙawayen su Uwani Nabila ta furta cikin zolaya, da yake a makaranta mafi yawa sunan da ake kiranta ita da Auta kenan. Jin sunan da aka ambata ya sa Safna ta ɗago ta dube ta, don babu tantama tun da ta ji inkiyar sunan Jafar ta fahimci ita ma Uwani ɗaya daga cikin 'yan uwansa ce. Sosai ta ga yanayin kamannin Uwani da na Auta, ta basar ta ci gaba da latsa wayarta. Murmushin yaƙe Uwani ta yi ta ce. "Sai kace babu manya a wurin zan bari ki karɓi haihuwata Nabila, wallahi kin ma raina ni da yawa." Yadda Uwani ke mu'amala da ƙawayenta a ɗan zaman da Safna ta yi haka kawai ra ji sun birge ta. Jakarta ta zuge da niyyar ɗaukan kuɗin liƙin da za ta yi wa Auta, ta dafe kanta sakamakon matuwar da ta tuna ta yi. Da sauri ta ciro wayarta ta latsa lambar Jafar, ba a ɗauki lokaci ba ya ɗauka. "Baby na yi mantuwa wallahi!" Daga can ɓangaren Jafar ya furta. "Me kika manta?" Saukar kalaman Jafar ya yi daidai da bugun ƙirjin Uwani da ke kusa da Safna, don tana jiyo maganarsa raɗau a kunnenta. Zuciyarta ta shiga harbawa da ƙarfi fat-fat. Wani irin kishinsa ya turnuƙe ta. Tana cikin wannan yanayin ta riski muryar Safna na faɗin. "Wallahi kuɗin da zan yi liƙi na manta a kan mirror." "Ni kuma kin ga yanzu na fito daga gida zan ƙaraso nan." A shagwaɓe Safna ta narke tana faɗin. "Please baby don Allah ka taho mini da su." Shiru Jafar ya yi sannan ya furta. "Sai na ƙaraso." Safna ta sake narkewa tana faɗin. "Don Allah Baby..." A hanzarce Uwani ta tashi daga wurin jin zuciyarta na barazanar tarwatse mata, a can kujerar da su Dada ke zaune ta ja wata ta zauna. Suna haɗa ido da Auta sakar mata murmushi, shiru Uwani ta yi tana jin zuciyarta babu daɗi. Idanunta ne suka ciko da ƙwalla, ta kwantar da kanta a jikin table a daidai lokacin Aunty ta ƙarasa wurin. Aunty ta yi kyau sosai gwanin birgewa, ɗagowar da Uwani ta yi ne ya sa Aunty ta fahimci tana cikin damuwa. Hannunta ta kama suka bar cikin mutane sannan ta ce. "Ina fatan dai ba jikin ba ne? Ko kin fara jin wani ciwon ne?" A madadin Uwani ta ba wa Aunty amsa sai hawaye ne ya fara bin gefen fuskarta, rungumo ta Aunty ta yi tana buga bayanta. Jin Uwani na kuka ya sa Aunty ta ɗago ta furta. "Yanzu so kike ki ɓata kwalliyar ta ki tun ba a gama taron ba?" Uwani ta girgiza kai ta ce. "Aunty ba ni key ɗinki zan wuce gida." Kallon tsaf Aunty ta yi mata ta sannan ta ce. "Kada dai saboda kishiyarki ta zo wurin nan kike zubar da ƙwallarki a banza? Uwani wai yaushe za ki yi wayo ki bar sakarcin nan?" Shiru Uwani ta yi Aunty ta miƙa mata tissuee sannan ta ci gaba da cewa. "Wallahi tun wani bai gani ba gara ki gyara fuskarki, salon a ga yanayin da kike ciki wani ya je ya kai mata rahoto ko? Ungo hoda maza gyara fuskarki ki wuce mu je, yanzu idan Auta ta ji kin wuce gida za ta ji daɗi ne?" Jiki a sanyaye Uwani ta karɓa ta shiga gyata fuskarta, sai dai har lokacin wani irin raɗaɗi take ci a cikin ranta. Aunty ta ci gaba da ƙarfafa mata gwiwa sai da ta saita nutsuwarta sannan suka koma cikin hall ɗin. Can filin da amarya take zaune Uwani ta nufa, wasu ƙawayensu na makaranta suka mara mata baya. Hotuna da video sauka shiga yi da amarya, sannan aka sakar musu kiɗa. A hankali Uwani take takawa, Auta ta sunkuya saitin kunnenta ta ce. "Maman baby wallahi na haƙura da rawar nan kada ki hautsina mini yarinya." Hararar wasa Uwani ta yi mata Aunty da ke gefe ta ce. "To sababbu a nan ɗin ma yi za ku yi?" Uwani ta saki murmushi ta ce. "Yarinyar kin ci sa'a yau ranar taki ce. Da ko hmmm." Uwani ta yi ƙwafa tana ci gaba da rawa. Uwani ta jima tana ɗan tattakawa sannan ta koma ta zauna, tana daga kujerarta take kallon yadda 'yan mata ke girgijewa. Tana zaune ta ji Mc ya ba da sanarwar amarya ta dawo cikin fili, zai lissafo sunayen mutanen da za su fito su nuna mata ƙauna. Murmushi Uwani ta yi don ta san duk salon samun kuɗin liƙi ne, bayan Auta ta fita cikin fili Mc ya kira sunan Shukra, Aunty, Mami sai ita. Duk da ƙafarta ta gaji hakan bai hana ta yunƙurawa da ƙyar ta miƙe ba, ta zaro kuɗi daga cikin jakarta bandir ɗin ɗari bibbbiyu sai na ɗari biyar guda ɗaya. Tun kafin ta ƙarasa Mami da Aunty suka fara yi wa Auta ruwan liƙi, ta yi mamaki sosai ganin yadda Mami ke sakar mata fuska tana yi mata murmushi, duk da ba wata doguwar alaƙa da ta shiga tsakaninsu amma ta ba ta girmanta na matsayin mahaifiyar mijinta. Uwani ta ƙarasa wurin a lokacin Aunty da Mami suka matsa gefe. Uwani ta ɓalle bandir ɗin 'yan ɗari biyar-biyar tana liƙawa. Aunty na tsaye ta hango Jafar shi da Safna sun tunkaro wurin, ita ma Safna hannunta ɗauke da bandir ɗin kuɗi. Aunty ce ta ƙarasa wurin Mc ta yi masa raɗa a kunne, tana matsawa ya saki wani sabon kiɗan yana faɗin. "An gaida Hajiya Hauwa'u mai hadarin nairori, wai na ce duk cikin filin nan Jiddah ce ce za ta nuna mata ƙauna ne? Ki taka lafiya Hajiya Maijidda, ni na san idan an haifo ɗan baby za a gayyoto ni nazo taya murna." Uwani ta saki murmushi tana ɗan tattakawa a hankali ta yi wa Auta ɓarin kuɗi ita ma Auta ta fara yi mata. "Allah sarki ita ma amarya ta ce ba za a barta a baya ba, kai da ganin waɗannan manyan matan ka san akwai ƙauna da zumunci mai ƙarfi a tsakaninsu. A gaskiya na yaba kuma ko gobe zan sake dawowa bikin ko sunan gidan Mai shanu" Wannan kirari da Mc yake yi ya ja hankulan mutane da dama, hakan ya sa wasu daga cikin 'yan biki suka fara matsowa cikin fili, kamar almara Jafar na kai idonsa wurin Auta karaf suka sauka a kan Uwani. Dam! Ya ji a saman kansa tamkar an kwaɗa masa guduma, Uwani jim bayanta ya gaji ya sa ta ɗago za ta bar cikin filin idanunta suka sauka a kan Jafar. Kusan mutuwar tsaye suka yi ƙirjinta ya shiga bugawa da ƙarfi, Auta ce ta lura da halin da take ciki ganin Jafar Uwani ke kallo ya sa ta saki ajiyar zuciya cikin farinciki don dama abin da take jira kenan. Ganin Jafar ya tsaya cak ya sa Safna ta waiga tana faɗin, "Baby mu ƙarasa mana." Da mamaki take bin sa da kallo, ta juya tana kallon wurin da yake kallo. Jikin Uwani ban da karkarwa babu abin da yake yi, cikin hanzari ta bi ta cikin rurumar mutane ta fice daga cikin filin. Kai tsaye ɗakin da suka ajiye gift ta faɗa tana jin zuciyarta na wani irin harbawa. Kamar zautacce haka Jafar ya fisge hannunsa daga riƙon da Safna ta yi masa yana faɗin. "Jiddah! Jiddah!" Sototo Safna ta yi da mamaki tana bin sa da kallo, ganin ya shiga cikin filin a haukace yana dube-dube da sunan da yake ambata. Cike da tsananin tausayi Auta ta bi shi da kallo har ya ƙarasa cikin filin, da yake Mc ya daɗa sakin wani kiɗan ya sa Jafar ya ja hannun Auta can gefe, jikinsa na rawa ya furta. "Ina Jiddah take?" Auta kamar ta yi masa bayanin Uwani sai kuma ta tuna alƙawarin da suka yi mata. "Ban san inda ta yi ba, amma da tana cikin wurin nan Ya Jafar?" "Amma kin san ta zo wurin nan shi ne ba ki sanar da ni ba?" Jafar ya tambaye ta a zafafe. "Zuwanta kenan Ya Jafar..." "Rufe mini ba ki." Jafar ya katse ta a hargitse yana ci gaba da dube-dube a haukace. Da Ido Auta ta bi shi da kallon tausayi, ganin ba shi da niyyar dawowa wurinta ya sa ta koma kujerar da aka tanada domin ta ta zauna a sanyaye. Da yake securites ɗin da ke gadin ɗakin da aka ajiye gift sun gane Uwani ya sa ba su dakatar da ita ba, don kusan ita ta bada umarnin duk yadda za a ajiye kayan ba tare da an hargitsa wasu ba. Uwani na shiga ɗakin ta turo ƙofa ta jingina a jikin ƙofar hawaye na bin fuskarta. Kuka take sosai saboda yadda zuciyarta ke yi mata, duk yadda ta so dakatar da zubar hawayenta abin ya ci tura. Sai da ta ci kuka mai isarta sannan ta warware ɗaurin ɗankwalin da aka yi mata, ta yafa mayafinta. Har za ta fita ta ɗauko waya ta kira Aunty, sai da ta katse har sau biyu sannan Aunty ta ɗauka. Sanar da ita wurin da take ta yi, babu jimawa Aunty ta ƙarasa. Ganin yanayin Uwani ya sanyaya mata jiki, don tun barin Uwani daga wurin ta lura da halin da Jafar yake ciki wanda hakan ne ya sa ta fahimci ya yi tozali da Uwani. "Aunty ki ba ni mukullin sashenki zan wuce gida." Uwani ta furta murya a dashe. "Ba zan bari ki tafi ke kaɗai ba, ki bari zan je na damƙa wa Shukra komai tun da dama an kusa tashi sai na dawo mu wuce gida. "Aunty ba na son Ya Jafar ya sake ganina ne." Da kallon tausayi ta bi Uwani ta ce. "Uwani mijinki yana sonki yana ƙaunarki, da za ki ga irin abin da yake yi a wurin can sai kin matuƙar tausaya masa. Ko kaɗan kada ki ƙullace shi ko ki ga laifinsa, abin da nake so da ke ki ci gaba da addu'a." Wasu zafafan hawaye suka sake zubo mata musamman da ta tuna yadda Jafar ya sako Safna a gaba suna tafe suna sakin murmushi. "Haba Aunty ta yaya za ki ce Ya Jafar na sona bayan ya samu wata ya manta da ni?" Uwani ta raya a ranka. Kamar Aunty ta san abin da yake cikin zuciyar Uwani ta furta. "Don Jafar ya auri wata matar ba shi yake nuni da cewar ya daina sonki ba, kamar yadda kike matarsa haka ita ma Safna matarsa ce. Ki ci gaba da addu'a Allah ya zaɓa abin da ya fi zama alheri." Wani abu mai nauyi ya sake danne zuciyar Uwani, ta amsawa Aunty sannan ta fice daga ɗakin. Haka Jafar ya gama karaɗe cikin hall ɗin da neman Uwani amma bai ganta ba, hakan ne ya sa ya nufi wurin da Dada ke zaune ita da ƙawayenta tsofaffi cikin wani irin yanayi ya ce mata. "Dada ina Jidda take?" Da mamaki Dada ta dube shi ta ɗan yamutsa fuska ta ce. "Wata ce kuma haka?" Jafar ya haɗe fuska ya ce. "Matata nake nufi tana ina?" Baki sake Dada ta ce. "To yaushe kuma matar so ta zama Jidda, wa take da suna Safya ko Safiya?" "Uwani nake tambaya wallahi ganin idona na ganta a wurin nan." Sai a lokacin Dada ta gane wacce yake nufi, ta yamutsa fuska ta ce. "Wani sabon munafurcin ka ƙullo Jafaru da ka sauya wa Uwani suna zuwa Jidda? Yo to don ka ganta sai me? Saboda kai za ta ƙi zuwa bikin 'yar uwarta ne?" Takaici ya sake mamaye Jafar ganin idanun mutane ya fara dawowa kansa, a lokacin Safna ta ƙarasa wurin cike da damuwa ta ce. "Baby lafiya wai me kake yi haka? Wace ce Jidda da kake neman tuburewa a kanta?" Jafar ya saki tsaki ya bar Safna da ke tsaye sororo, Dada ta riƙe haɓa jin sunan da Safna ta kira Jafar da shi. "Kai idan kana duniya za ka ga lalata iri-iri, ban da ɗaurewa iskanci wai Jafaru ake cewa Baby. Garsamemen ƙaton da zai iya zubar da maza biyar, Allah ya sawaƙewa lalacewar zamani." Safna ta gama kai wa wuya, don haka ta wuce fuuu ta bar wurin ba tare da ta tanka wa Dada ba. Tun da Aunty ta fita ba ta samu ta gama sallamar mutane ba sai gab da za a tashi daga hall ɗin, sai da ta damƙa wa Shukra duk abin da ya kamata sannan ta shiga wurin Uwani ta yi mata magana suka fita. A daidai kuma wannan lokacin Jafar na cikin motarsa ya ɗora kai asitiyarin motarsa cikin damuwa da ɓacin rai. Ta jima ta hangensa a cikin mota har suka wuce wani irin abu na yawo a cikin jikinta. Can titi suka fita suka tari adaidaita sahu suka wuce gida har lokacin Uwani ba ta daina jin zuciyarta na yi mata zafi ba. Lokacin da suka koma gidan babu kowa don haka suna zuwa sashen Aunty ta karɓi doguwarta mara nauyi bayan ta yi wanka ta saka, ta kwanta tana tunanin rayuwar da suka yi da Jafar a baya. Su Aunty sun jima da dawowa sannan sauran 'yan bikin suka dawo har da amarya. "Maman baby me ya sa kika son azabtar da ɗan'uwana? Me ya sa kike son horar da shi alhalin ba laifinsa ba ne? Wallahi-wallahi yau duk wanda ya ga abin da Ya Jafar ya dinga yi sai ya tausaya masa, me ya sa ba za ki saurare shi ko da na ɗan mintuna ba ne." Auta ta furta a sanyaye don ma'auratan ba ƙaramin tausayi suke ba ta ba. "Auta na san waye Ya Jafar, matuƙar zan tsaya saurararsa kema kin san ba zai taɓa bari na koma wurin Innata ba. Kuma ko Kur'ani zan haɗiya Dada ba za ta yarda da ni ba." Auta ta dafe kai cike da damuwa sannan ta furta. "Yanzu shi kenan haka za ku ci gaba da rayuwa? Na san abin da Mami ta yi sam ba ta kyauta ba, amma nake ganin yanzu ta gane kuskurenta. Me ya sa Dada ba za ta haƙura ki koma ɗakinki ba." Uwani ta sauke ajiyar zuciya ta ce. "Kin san an ce duk abin da babba ya hango yaro bai isa ya hango shi ba, addu'a dai ita ce mafita. Kuma wallahi ban ce ki sanar masa ina nan ba, idan ba haka ba na yi miki rashin mutumci." Auta ta taɓe baki ta ce, "Munafuka ji yadda take magana kamar gaske, da zan fallasa ki ai tuni a wurin zan faɗa masa. Tun da ni ce mutum ta farko da ya fara kira ya tambayi wurin da kike." Uwani ta yi murmushi ta ce. "Ki taɓo mini Aunty Shukra idan za ta tafi ni zan bita yau a gidanta zan kwana." Auta ta riƙe haɓa sannan ta ce. "Oh! Yau nake ganin ikon Allah ƙiri-ƙiri mata na gudun mijinta, ai shi kenan sai mu rankaya mu kwana a can. Na san gudunki dai kada ya zo nemanki nan." Uwani haka ta zauna a ɗakin Aunty don kada wani ya fitar da rahoton ya ganta a cikin gidan, sai da Shukra za ta wuce gida kusan goman dare sannan Auta da Uwani suka sulale jiki suka bita. Suna hanyarsu ta zuwa gidan Shukra Jafar ya sake kiran Auta yana tambayarta Uwani, ta ce masa ita ma da ta dawo gida ba ta ganta ba. Babu yadda ya iya haka ya katse wayar a lokacin yana harabar gidan Daddy, bayan ya yi aike ya fi goma a kan a gano masa Uwani a ɗakin Aunty. Jafar da ya runtse ido Uwani yake gani tana sakin murmushi tana yi wa Aura liƙi, tunani da fargabarsa a wurin da Uwani za ta kwana ga shi ga dukkan alamun da ya gani cikinta ya tsufa. Ya gagara fasalta irin kyawun da ya ta sake yi, ta sake zama babbar mace tamkar ba Uwaninsa ba. Ba shi ya koma gida ba sai kusan sha biyun dare, a lokacin da ya je Safna na zaune ta cika fam. Saboda tun a hall da Jafar ya fita ba ta sake ganinsa ba. Ko amsa sallamar da ya yi ba ta yi ba, yana shirin wuce ta da sauri ta sha gabansa. "Wacce 'yar gidan uban waye ta sha gabanka da har ka dizga ni kana ambatar sunanta a wurin Kamu." Kai tsaye Jafar ya ce. "Wata mai muhimmanci ce a rayuwata." Wani ashar Safna ta ƙunduma za ta sha gabansa ya janye ta gefe a shige ɗaki, ɗakin da yake ajiya kayan tarkacen aikinsa ya shiga tana shirin tura ƙofar ta ji ya saka sakata a jiki. Safna ta yi bugun dunjya Jafar ya yi banza da ita, cike da takaici ta koma ɗaki ta faɗa kan gado ta fashe da matsanancin kuka. A ranta ta raya za ta je ko gidan Daddy ko wurin dinner Auta, don ta ci alwashin a wannan karon ko wace ce sai dai a yi wacce za a yi a tsakaninta da ita. Washegari ne ya kama ranar dinner Auta, kuma Uwani ta ƙudure a zuciyarta ba za ta je ba. Lokacin da Shukra ta shirya za ta je gida ta ce su shirya su tafi Uwani ta ce ita za ta yi zamanta, Shukra ba ta takura mata ba ta shirya ta fita. Wurin sallar azahar ne Auta ta dawo gidan bayan ta je ta gano yanayin decoration ɗin da aka yi ita da Madina. Yamma liƙis ne kuma Auta ta ce wa Uwani ta shirya za su tafi wurin mai kwalliya amma fir ta ƙi yarda, ganin da gaske Uwani ba za ta ba ya sa ta kira Aunty kamar za ta yi kuka ta sanar mata. Aunty ce ta ce a miƙa wa Uwani wayar ai kuwa ta rife ta da faɗa, Uwani ta tura baki gaba ta ce. "Ni fa Aunty ba don komai ya sa na ce ba zani ba ɗan ciwo-ciwo nake ji kamar fa haihuwa zan yi!" Salati Aunty ta saki don ta gano ƙarya Uwani take ta ce, "To ki shirya idan haihuwar ta zo a hall ɗin sai na saka ki a ɗaki na karɓi haihuwar taki." Uwani ta saki murmushi don ta gane Aunty ta gano ta. Sai da Aunty ta yi wa Uwani da gaske sannan Uwani ta zumɓuri baki gaba ta suka shirya, abokin Dr ya zo ya ɗauke su suka wuce wurin make up. A wannan ranar wani narkakken leshi Uwani ta saka wanda aka yi mata ɗinkin doguwar rigar. Abinka da mai jiki ga kuma cikin jikinta ba ƙaramin kyau ta yi ba, ita kanta ta yaba da wankan da ta ɗauka don haka Auta ta shiga zolayarta. Jafar yana daga cikin mutanen farko da suka fara zuwa hall ɗin, don a wannan ranar ya ci alwashin ko sama da ƙasa za ta haɗe babu mai hana shi tafiya da matarsa. Bayan an gama yi musu make up Dr ya zo shi da abokinsa, suka ɗauki Auta da ta sha doguwar rigar tsadaddan lace-material. Ba ƙaramin kyau ta yi ba, Uwani kuma ta yi wa Shukra waya a kan ta biyo wurin make up ɗin, za su wuce su karɓo jakunkunan gift da suka bayar. Sai kusan bayan isha'i suka ƙarasa da yake sun tsaya ƙara wasu tarkacen kayan gift ɗin a ciki. A lokacin da suka shiga hall ɗin ya cika da mutane sosai, Uwani na zuwa ta ji an saki waƙar Mamana. Da sauri ta buɗe jaka ta fara yi wa Auta da Dr liƙi, Safna ko da ta je wurin tana lura da yanayin Jafar, uffan ba ta ce masa saboda koda gari ya waye ba ta tanka masa ba. Idanunta na kansa tana kallon yanayinsa da shige da ficensa. Yana daga zaune kamar an ce ya kalli wurin ya hango Uwani kamar dai jiyan, tana yi wa Auta liƙi tana ɗan jujjuyawa, wayarta ta ji tana ƙara da sauri ta ɗaga tana fita daga cikin filin. Muryar ƙawarsu Na'ima ta ji tana tambayarta kwatancan layin, don mai adaidaita sahu ya shiga layin hall ɗin da ita ba ta gane ba. Fita daga cikin hall ɗin Uwani ta yi tana yi mata kwatance saboda ƙarar ƙidan da ke tashi, hakan ya sa Jafar ya rufa mata baya jikinsa har rawa yake. Safna na ganin Jafar ya fita ta suri jakarta ita ma ta bi bayansa, don ta ci alwashin sai dai a yi wacce za a yi. Can wajen gate Uwani ta tsaya sai da ta gama yi wa Na'ima kwatancan layin da za ta shigo, waigowar da za ta yi idanunta suka sauka a kan Jafar da ke bayanta. Kallon-kallo suka fara wurga wa junansu kowannensu ƙirjinsa na bugawa, lokaci ɗaya jikin Uwani ya fara karkarwa. Abubuwa da dama game da mijinta suka bijiro mata, ta yunƙura da niyyar wucewa Jafar ya sa hannu biyu ya riƙo ta da iya ƙarfinsa ta faɗa jikinsa, ya riƙe ta ƙam tamkar wani zai ƙwace ta. Ɗago kan da za ta yi suka sake haɗa ido a karo na biyu, kusan lokaci ɗaya gabaɗaya suka sauke ajiyar zuciya sai kawai ta cusa kanta a cikin ƙirjinsa. Safna da ke baya kusan mutuwar tsaye ta yi ganin mijinta na rungume da mace. Jama'a magana ta gaskiya wanga wuri ya kusa sumar da ni, shi ya sa na gagara ƙarasa typing. Mu haɗe idan Allah ya kaimu🤭 Haɗuwar masoya kusan wata 9 is not easy🫠 Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank shaidar biya ta wannan no 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Mutsu-mutsu Uwani fara yi tana kiciniyar ƙwacewa ta sunkuyar da kanta a ƙasa, saboda kallon Jafar da ta yi na ɗan sakanni ne ya nemi tarwatsa ƙwarin gwiwarta. Sake janyo ta ya yi jikinsa ya yi ya sa hannu ya ɗago fuskarta suna fuskantar juna, wani abu Uwani take ji na ratsa ta tun daga tafin ƙafarta har tsakiyar kanta. Cikin wata irin murya Jafar ya furta. "Mene ne laifina da kike azabtar da gangar jiki da ruhina? A kullum kuma a kodayaushe na zama tamkar mahaukacin da ke turi, har ta kai mutane na yi mini kallon zautacce ko mai wata lalurar a kanki. Me ya sa kike nisanta kanki daga gare ni alhalin kin san ba zan iya jure rashinki ba, shin kin san adadin kwanakin da na yi ina bulayin nemanki? Kin san darare nawa na shafe ina mafarkin haɗuwa da ke? Kin san mutane nawa na dinga zuwa wurinsu ina cigiyar neman inda kika shiga?" Hawaye ne ya ciko idanun Uwani suka fara gangarowa ba tare da bin umarninta ba, Jafar ya sa hannu ya goge mata sannan ya kai hannunsa saman turtsetsen cikinta yana jin wani irin farinciki na ratsa shi. "Shin kema kin amince a raba mu kenan Jidda?" Kukan da Uwani ke riƙewa ne ya kwace mata, jin shasshekar kukanta ya sa Jafar ya rungumo ta a hankali ta fara sauke ajiyar zuciya. "Ina sonki ina matuƙar ƙaunarki, na yi kewar wannan bakin tsiwar taki. Na yi kewar komai na ki, a kullin ƙaunarki ke nashe mini zuciya. Ko ba za ki amsa mini ba don Allah ki furta mini kalma guda da za ta sanyaya mini rai, ko zan samu sauƙin dafin da ke kwance a zuciyata Jidda." Aunty da tun fitowar Uwani ta biyo bayanta don ta yi tsammanin Uwani tafiya za ta yi, ta goge ƙwallar da ta taru a idonta. Don Jafar da Uwani ba ƙaramin tausayi suka ba ta ba. Jafar ya haɗa hannuwansa biyu alamar roƙo sannan ya cigaba da cewa. "Don Allah Jidda ki taimaki zuciyata da ke barazar tarwatsewa." Uwani ta goge ƙwallar fuskarta ƙirjinta na bugawa, cikin tsantsar soyayya da kewar mijinta wani ta furta. "Ina ƙaunarka Nur domin soyayyarka a cikin jinin jiki da ruhina take yawo." Uwani na gama maganar ta bi ta gefensa za ta gegare shi ta wuce. Safna da ke tsaye tun farkon fitowar Jafar ta fisgo Uwani da ƙarfin tsiya cikin tsananin kishi ta ɗauke ta da mari haɗe da hankaɗa ta da iya ƙarfinta. Bi sa tsautsayi Uwani ta bugu da jikin gate ɗin Hall ɗin ta faɗi a ƙasa, wata irin azaba ta ji a cikinta har zuwa mararta don haka ta ƙwalla wata irin gigitacciyar ƙara. A haukace Jafar ya shaƙo Safna ya wanke ta da zafafan mari, idanunsa a rufe saboda ɓacin rai ya rufe ta da wani mahaukacin duka. Aunty da ƙawarsu Uwani Na'ima da ƙarasowarta kenan suka yi kan Uwani suna salati. "Wayyo cikina! Innalillahi wa inna'illahir raji'un! Wayyo marata." Uwani ta furta cikin tsananin azaba. Wasu Police da ke jikin gate ɗin hall ɗin a tsaye ne suka ƙwace Safna daga hannun Jafar ganin yana neman illatata, a haukace ya yo kan Uwani yana kiran sunanta. Ganin halin da take ciki ya sa Jafar ya kinkime ta ya saka ta a motarsa. Kafin wani lokaci tuni 'yan biki sun fito waje carko-carko jin labarin abin da ya faru, Aunty da Shukra ne suka shiga bayan motar da Uwani ke kwance cikin galabaita. Jafar gudu yake kamar zai tashi sama a haka suka ƙarasa wani private hospital da ke titin state road. Da zuwansu babu jimawa aka shiga da Uwani domin ba ta agajin gaggawa, Dr Sadik ne ya fito yana sharce gumi Jafar na ganinsa ya ƙarasa wurinsa. "Ya ake ciki Dr? Zan iya shiga na ganta?" Girgiza masa kai Dr Sadik ya yi ya ce. "Yanzu haka za ka yi signing ne saboda dole sai dai mu yi mata aiki mu ciro abin da yake cikinta." Aunty da Shukra jin haka ya sa jikinsu ya sake sanyi, Aunty ban da kuka babu abin da take yi. "Dr zan yi indai za ta samu lafiya a ciro babyn. Don Allah ka taimaka mini wallahi ina ƙaunar Jidda!" Jafar ya faɗa cikin tashin hankali. "Ka kwantar da hankalinka In Shaa Allahu za mu yi mata aikin cikin nasara, fatan dai ku yi mata addu'a ba kuka ba kamar yadda na ga sisters ɗinta suna yi." Wayar Aunty ce ta fara ƙara sai da ta share hawayenta sannan ta ɗauka. "Zainabu a wanne asibitin kuke?" Daddy ya furta daga can ɓangaren, da yake a ruɗe take sai da ta tambayi wata nurse sannan ta yi masa kwatancan asibitin. Jafar na gama signing aka shiga da Uwani ɗakin tiyata, Jafar ban da kaiwa da kawowa babu abin da yake yi. Mami ce ta kira shi a waya ta tambaye shi asibitin da suke, Jafar ya kwatanta mata ta ce masa gata nan zuwa. Bayan wani lokaci Dr Husna ta leƙo fuska ɗauke da fara'a, suna ganinta gabaɗaya suka yi wurinta suna jera mata tambaya. "AlhamduLillah! Mun samu nasarar yi mata aiki, kuma ita da baby suna cikin ƙoshin lafiya." A take Jafar ya tsugunna ya yi sujjada, a daidai wannan lokacin Daddy ya ƙarasa hankali a tashe. Yana zuwa ya samu kyakkyawan labari, cikin farin ciki ya shiga ɗaga hannu yana godiya ga Ubangiji. Mami ce ta yi sallama jiki a sanyaye kamar kazar da ta taka wuƙa, ko kallon kirki Aunty ba ta yi mata ba. Jafar ta tambaya jikin Uwani nan yake sanar da ita haihuwar Uwani. Sai dai likitoci sun tabbatar musu sai an gama gyara ta da jaririn za a kai su ɗakin da kowa zai iya shiga ya gansu. Jafar saboda farin ciki ya kasa zaune ya kasa tsaye ji yake kamar ya yi tsuntsuwa ya faɗa ɗakin, yana nan tsaye ya ciro wayarsa. Misscall ɗin Auta ya gani rututu yana shirin kiranta ya ji Aunty na waya da ita. "AlhamduLillah an yi mata aiki ita da babyn suna cikin ƙoshin lafiya, eh sun ce namiji ta haifa." Ihu Auta ta saki ta ce gata nan zuwa, don dama tun bayan abin da ya faru da Uwani babu jimawa aka tashi daga dinner. "Am yanzu za ku iya shiga ku ganta kafin mu yi mata allurar bacci, but please ba ta buƙatar hayaniya da yawa. And ba ma buƙatar a daɗe saboda tana buƙatar hutu." Dr Sadik ya furta yana nuna musu wani ɗaki da ke kallo su, Jafar bai tsaya jin ta bakinsa ba ya nufi ɗakin cikin sauri. A kwance ya same ta da jaririnta a gefenta, wani irin farin ciki ke ratsa shi ya ƙarasa bakin gadon ya sumbaci goshinta. "Yanzu wannan ɗana ne Nue?" Jafar ya furta da wani irin yanayi, murmushi Uwani ta sakar masa, ya riƙo hannunta ya sumbuta yana jera mata sannu. Jaririn ya ɗauka ya rungume shi tsam yana jin soyayyarsa a cikin ransa, tabbas ko makaho ya shafa fuskar jaririn sai ya tabbatar da matsananciyar kamar da suke yi. A haka su Daddy suka ƙarasa ɗakin, suka karɓi jaririn suna yi wa Uwani sannu. Wani irin nauyinsu take ji don haka ta gagara haɗa ido da su, jaririn sai tsotsar hannu yake. Daddy ya ƙura masa ido yana sake jaddada godiyarsa da Ubangiji ya nuna wa Mami ranar da Uwani ta sauke cikin Jafar. "Zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzuru ana shaho sai ya yi, tabbas duk abin da ka ga Ubangiji ya ƙaddara ya fi mu sanin alkairinsa a gaba. Yau dai ga jinin Jafar ya fito ta jikin Uwani kai Allah mun gode maka." Aunty ta yi maganar cikin farin ciki. Jikin Mami ba ƙaramin sanyi ya yi ba, wata irin kunya ta kamata. A kunyace ta ƙarasa ta ƙarɓi jaririn tana jin soyayyarsa a ranta, ta ƙura masa ido ta kallon zallar kamar da su da Jafar. Ba su jima ba suka fita suka bar Jafar a ɗakin kowanne zuciyarsa fal da farin ciki, a kujera Jafar ya zauna a matsa kusa da Uwani ya riƙo hannunta yana jin ƙaunarta a zuciyarsa. "Ya Jafar me na yi wa matarka da take yunƙurin hallaka rayuwata da ta abin cikina?" Uwani ta furta a hankali. "Shiiiii ba na son jin komai yanzu, kin ga jikinki babu ƙwari ko kina son ki sa wa kanki damuwa?" Jafar ya yi maganar kamar da ƙaramar yarinya yake, Uwani ta girgiza kai sannan ya ce. "Na yi waya da wani yarona Sargent Musa yanzu haka tana can a hannunsu, ki kwantar da hankali kin ji Jiddona." Gyaɗa masa kai Uwani ta yi yana nan zaune wasu Nurse suka shiga, suka buƙaci da ya fita za su yi mata allurar bacci. "In dai nine ba ku da damuwa zan zauna na kula da baby." Jafar ya furta yana sake rungume jaririn, murmushi ɗayar ta yi ganin yadda yake ƙara riƙe babyn gam kamar wani zai ƙwace masa shi. Yana nan zaune aka saka wa Uwani allurar a cikin drip tun Nurse ɗin na cikin ɗakin wani bacci mai daɗi ya yi awon gaba da ita. Su Mami suna zaune a reception kiran Hajiyan Safna ya shigo wayarta, gabanta ne ya faɗi jiki na rawa ta ɗauki wayar ta matsa can nesa daga cikinsu Aunty ta nufi ƙofar fita. "Hello Hajiya..." "Dakata! Babu wani abu da za ki faɗa mini, azzaluma macuciya. Ashe dama munafurtata kike Saratu ban sani ba sai yau da Allah ya tona asirinki? Wallahi kin ba ni mamaki. Ashe mu kika mayar 'yan iska da ba ki taɓa sanar mana Jafar yana da mata ba shekara da shekaru, to ga ɗanki nan ki kwaɗa shi ki cinye wallahi ko shi ne autan maza Safna ta haƙura da shi. Munafukar banza kwaɗayayya..." A zafafe Mami ta katse Hajiyan Safna don kalamanta ba ƙaramin ɓata mata rai suka yi ba. "Ke tsaya Rakiya ni ma fa ba tsoronki nake yi ba, an ƙi a gaya miki yana da matar ke kin biyo ta sigar da za a faɗa miki hakan ne? Jafar ɗana ne ko yanzu na so ya sauwaƙe wa Safna sai ya sake ta, Allah na tuba ma ban da ƙaddara ina ni ina haɗa zuri'a da ke..." "Iyeee ni kike faɗa wa haka Saratu? Wallahi kin yi da 'yar halak. Ni ban ce ƙaddara ce ta sa 'yata auran ƙaramin ma'aikaci kamar ɗan sanda ba sai ke? Kin san dai duk tsiya koda girgiza kurna ta fi magarya, nesa ba kusa ba Safna ba ajin Jafar ba ce. Don ma jaraba irin ta ɗan yau da ka haife shi ba ka haifi halinsa ba, wallahi Saratu da ni kike zancan kuma duk wata dukiya da kika san na damƙa miki ki dawo mini da abata, tun da ba ƙira babu abin da zai ci gawayi." Jin kalaman Hajiyan Safna na ƙarshe ya nemi ɗaga wa Mami hankali, don ta san ba ta da kafar da za ta biya ta maƙudan kuɗi da ta dinga karɓa a wurin Hajiyan Safna, koda kuwa tana gidan Daddy ne ballantana da a yanzu babu wasu kyawawan kuɗi da suke shigo mata. "Haba Hajiya wannan fa ba wani abin ɗaga hankali ba ne..." "Saratu kada ki raina mini hankali, kin san dai ni ba sa'ar ƙawancenki ba ce ko? Zumuncin yara ne ya haɗa mu kuma ya raba don haka babu wata magana da za ki faɗa mini a yanzu." Daga haka Hajiyan Safna ta katse wayarta, Mami ta yi mata kiran duniya ta ƙi ta ɗauka. Lokaci ɗaya damuwa ta cunkushe kwanyar Mami, nadamar kwaɗayi da son zuciyar da ta bi ya mamaye ta. Jiki a sanyaye kamar akuyar da ta bi ta mahauta ta koma cikin su Aunty ta zauna, zamanta babu jimawa Dada da Baba Mustafa suka ƙarasa cikin asibitin, a wulaƙance Dada ke bin Mami da kallo don tun da ta ji abin da ya faru ta ɗora laifi a kan Mami. "Saratu me kike zo yi wurin jikata kuma? Ina 'yar so ɗin ai na ɗauka za ki bi ta a rufe ku tare?" Dada ta furta cike da takaici. Shiru Mami ta yi ta sunkuyar da kanta ƙasa, Dada ta wuce tana sakin tsaki. Jafar ne ya fito ya miƙa mata jaririn Dada ta karɓa tana zuba wata kabbara da har sai da ta bawa Nurse ɗin da ke kai kawo a wurin dariya. "Mamman maza kira mini Maryama na shaida mata ta yi ango." Daddy ya yi murmushi ya ce. "Wallahi na kira ta Dada amma kin san Maryama da kunya ce wa ta yi tun da muna wurin shi kenan." Dada ta riƙe haba sannan ya miƙa masa wayarta ta sa ya kira mata ita, Sai da suka gaisa Maryama ta yi wa Dada barka sannan Dada ta fara yi mata faɗa. Da ƙyar dai Innar Uwani ta amince za ta zo washegari ta duba jikin Uwani. Zuri'ar gidan Mai shanu ba su suka bar cikin asibitin ba sai kusan karfe goma ɗaya na dare, Aunty ce ta zauna a wurin Uwani ai kuwa kafin Jafar ya yarda sai da Daddy ya yi masa fata-fata. Saboda cewa ya yi shi zai zauna ya kula da ita, ko da ya koma gida hotuna da videos ɗin jaririn ya dinga kallo cikin farinciki. Tun bayan tafiyar su Uwani asibiti wasu yaran Jafar suka wuce da Safna can Bompai, kuma koda suka wuce da ita babu ɗigon nadama a tattare da ita. Cike da shagwaɓa ta kira Mami da Daddynta ta sanar da su abin da yake faruwa, Mami ranta ba ƙaramin ɓaci ya yi ba. Daddy ne ma ya rife Safna da faɗan dukan da ta yi wa Uwani da ciki. Waya Daddy ya ɗauka ya kira wani babban ma'aikacin Ɗan sanda domin a sakar masa 'ya, tashin farko aka tabbatar masa da ba shi da ikon da zai sa a sake ta tun da zarginta da ake da laifi kuma kai tsaye Safna ta amsa laifinta. Sai dai idan har zai bari zuwa washegari ya je ya yi belinta. Kuma abin da ya sake ɓata ran 'yan sandan bai wuce yadda Safna ta dinga iƙirarin mahaifinta zai iya tuɓe ma'aikatan da suka kai ta can babbar Hedikwar hukumar 'yan sandan ba. Mami da kanta ta sa Jafar ya yi mata jagora har zuwa wurin Safna washegari, saboda furucin maifiyarta ya ɗaga hankalin Mami. Sam bai so hakan ba don dai Mami ta matsa masa amma ko sunanta ya tuna ransa ɓaci yake yi. Ta jikin ƙarfen cell ɗin Mami ta leƙa fuska ɗauke da damuwa ta ce, "Sannu Safna!" A wulaƙance Safna ta dube ta sannan ta ce. "Me ya kawo ki wurina? Ki adana kalamanki Malama domin komai ya faru ke ce sila, tun da ke kika munafurce mu ni da mahaifiyata." "Ba ki da hankali mahaifiyata kike faɗa wa haka?" Jafar ya faɗa a tsawace. "Na faɗa mata, munafiki azzalumi maha'inci, mayaudari." Safna ta furta cike da tsiwa. Jafar zai sake magana Mami ta dakatar da shi ranta a ɓace, suna na shirin fita sai ga Hajiyar Safna ta ƙarasa ita da wani ƙanin Daddy kasancewar mahaifin Safna ba ya ƙasar. Sai da Hajiyan Safna ta ƙare wa Mami zagin tsamar nama sannan suka ƙarasa ciki, suka yi duk cike-ciken da za su yi sannan aka ba su belin Safna. Ko da suka fito Jafar da Mami na shirin tafiya Safna da mahaifiyarta suka sake ɗorawa da wani zagin, a wannan karon ran Jafar ba ƙaramin ɓaci ya yi ba. Hajiyanta na shirin tasa ta a gaba su wuce gida Jafar ya miƙa mata takardar saki. Duk wani rashin mutumcin da ke kan Safna a daidai wannan lokacin sai da ya sauka, sakamakon ido biyu d ta yi da abin da yake rubuce. Jiki na rawa zuciyarta na bugawa ta dube shi. "Ni ka saka Jafar?" Jafar bai tanka wa Safna ba ya buɗe wa Mami mota ta shiga, shi ma yana shiga ya tashi motar ya fice daga cikin Hedikwatar zuciyarsa na zafi. Ganin haka ya sa wasu tagwayen hawaye suka fara bin fuskar Safna, Mummynta ce ta rungume ta tana share mata hawaye sannan ta ƙarfafa mata gwiwa suka wuce gida. Kwanan Uwani uku a asibiti aka sallame ta saboda jikinta ya yi kyau, kai tsaye Dada ta ce za ta wuce da Uwani wurinta a nan kuma Jafar ya kafe kai da fata a kan ba zai bar matarsa ta bi Dada ba. Sai da Daddy ya yi masa da gaske sannan ya amince, ranar kuwa da aka mayar da Uwani Kura shi ma Jafar a cikin gidan ya kwana, don gani yake idan ya tafi kamar Uwani za ta sake guje masa. Mami da kanta ta kira Daddy ta sanar da shi maganar sakin Safna, don ta samu a yanzu Daddy na sauraronta idan ta kira shi a waya. Ran Daddy ya ɓaci matuƙa, kuma a nan take ya kira Jafar don ya ji daga bakinsa. Ba ƙaramar kulawa Uwani take samu a wurin Dada ba, haka daga ɓangaren Jafar wani abin da yake yi musu ita da babyn har kunya take ci. Sunan mahaifin Uwani aka saka masa don haka suke kiransa da Hibban, hankalin Jafar ba ƙaramin kwanciya ya yi ba ganin Uwani na zaune daram a wurin Dada. Abu ɗaya ne yake damunsa da Dada korarsa da take yi da zarar ya shiga wurin matarsa, sai ta dinga ce masa miji ba ya zuwa wurin mace idan tana jego sai dai kallo daga nesa. Ranar da Uwani ta cika kwana goma da haihuwa Jafar ne ya shiga ɗakin a lokacin Dada ba ta nan, a zaune ya samu Uwani ta gama shayar da Hibban. A kusa da ita ya zauna bayan ta amsa sallamarsa ta furta. "Ina wuni Nur?" Jafar ya shagwaɓe yana faɗin. "Ba zan amsa ba! Jidda yanzu biyewa Dada za ki yi ta dinga hana ni ganinki ina jin ɗuminku?" Shiru Uwani ta yi tana murza hannunta don ita kanta idan ta ce ba ta yi kewar mijinta ba ta yi ƙarya. Janyo Uwani ya yi jikinsa cike da shauƙin so da ƙauna, ajiyar zuciya Jafar ya sauke yana jin ƙaunarta na fusgarsa, sake janyo ta ya yi ya fara yi mata raɗa a kunne haɗe da sakar mata kisses. Lumshe ido Uwani ta yi tana jin ƙaunar Jafar a ranta, suna nan a haka suka ji motsin Dada. Da sauri Uwani ta fara kiciniyar ƙwace kanta cikin jin kunya ta furta. "Ya Jafar Dada za ta shigo!" Idon Jafar a lumshe ya furta. "Zunubi na aikata ko me?" Dada na ƙarasawa wurin ƙofa ta fara hasko su da touchlight tana faɗin. "Wai ni motsin me nake ji a cikin ɗakin nan ne? Abu kamar munafurci har da sauke labule su waye a ciki?" A wannan karon ma Uwani ta so ƙwace kanta Jafar ya matse ta, Dada na shiga ɗakin ta ƙanƙance ido ganin Uwani rungume a jikin Jafar ya sa ta wurgar da touchlight ɗin hannunta tana rafka salati. Jafar ya gimtse daryarsa ya yi kamar bai ga Dada ba ya ɗago Uwani ya haɗe bakinsu wuri ɗaya, idonsa a lumshe ya ɗago yana faɗin. "Jiddana kin ga tun da Dada hana ni zuwa take yi wurinki a ɓoye ba sai na dinga ɗaukanki muna fita daga gidan ba. Ni fa na yi kewarki Jiddana, kuma na lura Dada so take ta wargaza sunnar Ma'aiki." Jafar ya furta cikin kwaikwayon kalaman Dada, ya ɗan waigo ya ga yadda Dada ta dafe ƙirji hannuwa bibbiyu ya sake gimtse dariyarsa ya cigaba da cewa. "A gaskiya ba zan iya jira har sai kin yi kwana arba'in za ki koma wurina ba. Idan kuwa Dada ta tsaurara tsaro sai ki haife mata ƙanin Hibban a gabanta." Dada na jin haka sai kawai ta fashe da kuka ta ce. "Jafaru dama abin da yake kawo ka ɗakina kenan? Munafiki algungumi ashe huɗubar tsiya kake yi 'yar mutane shi ya sa idan na kore ka sai Uwani ta ɗauki fushi da gaba da ni." Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank shaidar biya ta wannan no 07062062624 idan littafi ya kammala 800 ne.🫠 #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Murmushi Jafar ya saki jin kalaman Dada ya waiga wurin Dada sai kuma ya haɗe fuska yana faɗin. "Dada wai dama kin shigo ne?" Dada ta riƙe baki ganin har lokacin Jafar na riƙe da Uwani ta ce, "Ina za ka san na shigo kana nan kana hurewa 'yar mutane kunne. Yanzu wannan wacce irin jarabar duniya ce Jafaru yarinya ko sati biyu ba ta yi da haihuwa ba, za ka saka ta a lungu kana naniƙa?" Jafar ya sake tsuke fuska ya ce. "Wai Dada me ma ya shigo da ke alhalin kin ji miji da mata ne a ciki. Yanzu kuma idan kika gano wa idonki ki ce wa Ubangiji me?" Takaici ya sake rufe Dada ta kai wa Jafar duka a baya tana faɗin. "Don ƙaniyarka ka zo ɗakina ƙiri-ƙiri ka ce mini na gane wa idona. Wallahi bari Mamman ya zo ba zan iya ba, na lura Jafaru so kake ka kai ni wuta ban shirya ba. Yanzu idon na ganowa idona tsiraici na ce wa Ubangiji me?" Dada ta ƙarasa maganar tana kallon Uwani da ta yi luf a jikin Jafar. "Munafuka ashe dama kallona kawai kike Uwani, shi ya sa kika ɗaukar fushi da ni idan na kori Jafaru. To ki je don kanki wallahi indai Jafaru ne ina zaune za ki sake kwaso wani cikin." Ganin su duka biyun sun yi wa Dada shiru ya sa rai a ɓace ta juya tana kuka za ta fita, da sauri Jafar ya ƙarasa ya rungumo Dada ya dawo da ita suka zauna. "Haba Dada me ya sa kike haka ne? Yanzu laifi ne don na zo ganin matata? Ke da kanki fa kin san laifin mai ƙoƙarin tarwatsa sunnar Ma'aiki." Shiru Dada ta yi tana nazari sannan ta ce. "Ni fa duk ba wannan ba, Allah Ya sani tsoro kake ba ni Jafaru, haka kawai ka zo ka sake ƙunsa wa 'yar mutane ciki a ɗakina ina na kama?" Murmushi Jafar ya yi ganin ya fara cin galaba a kan Dada sannan ya ci gaba da yi mata daɗin baki. Satin Uwani biyu da haihuwa aka yi taron suna, saboda aikin da aka yi mata. Ita da jaririnta sun yi kyau gwanin birgewa, su Aunty sai shige da fice take. Jafar ma bakinsa har kunne don ya lura Dada ta gama huce fushinta, tun da har ya ji tana maganar Uwani za ta koma bayan ta yi kwana araba'in. Auta amarya tun sassafe ita da Shukra suka dira garin Kura, Dada ba ƙaramin mamakin sauƙin kan Shukra take ba. Madina kuwa sai da ta biya ta wurin Mami wurin azahar sannan suka ƙarasa, Mami ta yi ƙoƙari matuƙa wurin haɗa kayan barka don shi kansa Jafar bai taɓa tsammani daga gare ta ba, musamman yadda ya san ta ɗauki karan tsana ta ɗora wa Uwani. Taro ya yi taro gwanin birgewa, dangin mahaifiyar Uwani su kansu sun yi rawar gani wurin haɗo mata sha tara ta arziƙi. An ci an sha an yi hotunan cikin farinciki, facalolin Mami sai mamakin sauyin halin Mami suke yi da sauƙin kanta. A haka har aka yi taro aka gama kowa ya watse, gida ya rage sai tsirarun baƙin da suka zo daga nesa. Abin duniya ne ya haɗe wa Safna sakamakon ganin yadda Jafar ya yi watsi da ita, tun tana sa ran ganin ya biyo gidansu ya zo biko ya mayar da ita har zuciyarta ta fara wasu-wasin kiransa a waya. Momynta ce take tausarta amma duk da haka ciwon son Jafar da shi take kwana take tashi, lokaci ɗaya Safna ta zabge ta yi wata irin rama. Ta shiga tariyo abubuwan da suka faru a zamantakewar aurensu da Jafar, haka kawai take zama ta ci kuka ta more idan abin ya dame ta. A cikin hakan ne ta fara rashin lafiya da ciwon kai mai zafi, zuwansu asibiti likita ya tabbatar wa da Mommynta hawan jini ya kamata kuma ciwon zuciya na barazanar kama ta. Hankalin iyayenta ba ƙaramin tashi ya yi ba sakamakon ita kaɗai gare su, a wannan lokacin ne kuma Mummynta ta ta yanke shawarar kiran Mami domin su sasanta, saboda Safna ko ta kira Jafara ba ya ɗauka. Idan kuma baƙuwar lamba ta sa ta kira shi da ya ɗaga idan ya ji muryarta ce sai ya katse. Wannan ta sa mahaifinta ya shirya ƙafa da ƙafa ya je ya samu Daddy, sai da ya gama zayyano jawabi cike da mamaki ya ce. "Yaron nan ashe raina mini hankali ya yi da ya ce mini ya je wurin Safna sun gama daidaitawa? Alhaji ka yi haƙuri, kuma a gaskiya ya kamata ku sake lura da irin tarbiyyar Safna. Ba wai don Uwani tana 'yar ɗan uwana ba, wallahi da ace wata aka yi wa haka iyayenta ba za su amince ba. Kuma duk lalacewa mahaifiyar mijinta ai mahaifiyarta ce. Zan yi ƙoƙarin ganin na shawo kan Jafar ya mayar da ita, amma kuma matuƙar za ta dawo da halayenta magana ta gaskiya ba kowanne miji ne zai zauna da ita ba." Jinjina kai Mahaifin Safna ya yi don shi kansa ya fahimci kuskuren da suka tafka dangane da tarbiyyar Safna, soyayyarta ce ta rufe musu ido ya sa idan ta yi wani abin ba sa iya tsawatar masa. Sai da ya yi wa Daddy godiya sosai sannan suka yi sallama ya wuce gida. Bayan tafiyar mahaifin Safna ne Daddy ya kira Jafar ya ce yana son ganinsa cikin gaggawa. Lokacin da ya ƙarasa gida Daddy ya yi masa faɗa sosai sannan ya ce masa ya dawo da Safna. "Daddy ka yi haƙuri amma gaskiya ni na gama zama da Safna, ba zan iya zama da matar da take neman illata iyalina ba kuma tana cin zarafin iyayena ba." Shiru Daddy ya yi sannan ya ce. "Ya kamata ka ba ta dama a wannan karon tun da na tabbata a yanzu ta gane laifinta." "Ko zan dawo da ita Daddy ba yanzu ba, sai nan da wani lokacin In Shaa Allahu." Amsa masa Daddy ya yi sannan ya sallame shi. Wanka ya karɓi Uwani ba ƙaramin kyau ta yi ba, ta yi haske sosai ita da Hibban ba ƙaramin kulawa suke samu. Jafar kusan kullin yana hanyar Kura, wani abin da yake yi a kanta da Hibban a gaban mutane har kunya Uwani take ji. Sannu a hankali kwanaki suka shuɗe har ta yi arba'in, kuma a wannan lokacin tuni an gyara wa Uwani sashenta da ke gidan Jafar saboda tariyarta. Duk yadda Jafar ya dage a kan shi zai kai Uwani yawon arba'in ƙin yarda Dada ta yi, haka Dada ta fara saka su Baba Mustafa da Baba Yunusa suka dinga kai ta wurare suna dawo da ita. Wata unguwar kuma da babu nisa sai su tafi tare da Dada, duk inda suka je sai an yaba yadda Hibban ya yi ƙiba kamar ba jaririn kwana arba'in ba. Dada da Aunty ne suka yi wa Uwani duk wani abu da ya shafi ɓangaren gyaran jiki na mata, kuma a wata ranar Asabar ne aka raka ta ɗakinta. Uwani har da kukanta lokacin da su Dada za su tafi. Baki sake Dada ta dubi Uwani ta furta. "Wallahi idan ba ki rufe mini ba ki ba Uwani sai na dalla miki mari, kinibaye mu za ki yi wa bariki ki cuce mu muna zaune ƙalau? Wani sabon munafurcin kika tarko Uwani, ina ce haka Jafaru zai bi ki har ɗakina ya gama matse ki har idan na kore shi ki dinga gaba da ni. Amma shi ne yanzu za ki ɓarke mana da kuka, uban me za ki yi wa kuka to?" Uwani ta tura baki ta ce. "Dada wallahi zan yi missing ɗinku?" Dada ta yamutsa fuska ta ce, "Au dama musun ɗin har tsofaffi ake faɗawa? Wani abu ne haka?" Aunty ta yi dariya ta ce. "Dada tana nufin fa za ta yi kewar mu." Jin haka ya sa Dada ta ɗauki Salati tana tafa hannu sannan ta ce. "Wai dama musun ɗin kewa kenan? Shi ya sa kullin Jafaru ya zo sai na ga Uwani ta maƙale kafaɗa kamar keken ɗinki tana cewa ta yi musun ɗinsa, wallahi ke dai an yi baƙar munafuka. Ashe ke kike yaudaro Jafaru ki ribato shi nake ganin laifin yaro, saboda lalacewar zamani Abuwa shi ma fa haka za ki ji Jafaru yana kashe murya idan yana yi mata magana. Ke ni wani lokacin ko maganarsu ba na ji a ɗaki sai dai fa na ji ƙusur-ƙusur, kuma idan na faɗa ɗakin su ga laifina. Don Allah mene ne laifina don na duba na ga halin da suke ciki tun da Uwani dai amanar Allah ce a hannuna." Aunty ban da dariya babu abin da take yi, kunyar duniya ya cika Uwani. Horn ɗin Daddy suka ji a ƙofar gida ya sa suka yi wa Uwani sallama suka fita, har bakin gate ta raka su tana shirin tura ƙofa Jafar ya kawo kai hannunwansa ɗauke da ledoji guda biyu. Ledar hannunsa ɗaya ta karɓa, ya sakalo ta suka wuce cikin gida yana jin farincikin da ko da aurensa da Safna bai yi zumuɗin ranar ba. Suna shiga falo Jafar ya wuce kitchen ya ɗauko plates ya fara juye sayayyar da ya yo musu, Hibban ne ya fara motsi Uwani ta ɗauke shi. Jafar ya karɓe shi ya fara jijjjiga shi, jin ya ƙi daina kuka ya sa ta karɓe shi ta ba shi ya sha. Bacci ya koma sannan ta kwantar da shi ta tofe shi da addu'o'i, tana ɗagowa Jafar ya rungomta ya haɗa ta da bango. Iska ya hura mata a fuska cikin shauƙi ya furta. "Ban san da wanne suna ya dace na kira wannan ranar ba, amma Allah Ya sani zuciyata na cike da kewa da matsanancin farinciki." Shiru Uwani ta yi ta ɗan sunkuyar da kai ƙasa don haka kawai take jin nauyin Jafar, ɗago da fuskarta ya yi ya kashe mata ido ɗaya ya ce. "Jidda wai kunyata kike ji? Ina duk missing ɗin da ake cewa an yi ko duk faɗa ne?" Murmushi Uwani ta yi ta ce. "Da gaske ne mana!" "Ni ban ga alama ba, tun da dama kin bar ni haka kamar maraya." Jafar ya yi maganar da alamar tausayi, ba ƙaramin dariya ya ba ta ba. A hankali ya fara aika mata sakwanni, a kunyace Uwani take mayar masa da martani. Ganin Jafar na neman mayar da lamarin babba ya sa ta ɗan janye jikinta tana faɗin. "Ya Jafar mu je mu ci abinci ko?" Idonsa a lumshe ya furta, "Da fatan dai kin sallami little Papa don kada ya hana ni rawar gaban hantsi. Don gaskiya yau dole ya ɗaga miki ƙafa ki ji da Papa." Jafar ya kashe mata ido bayan ya ɗago. Rufe baki Uwani ta yi tana dariya ta ce. "Wallahi Ya Jafar nema kake ka fi ƙarfina, ni kam yaushe idonka ya sake buɗewa haka." "Wallahi duk yadda na zama ke ce sila, haka kawai aka ɗauko ni aka damƙa miki amana ina salihina, amma ƙiri-ƙiri kina neman lalata ustazun Daddy." Uwani ta zaro ido waje cikin wasa tana dariya ta ce. "Ai shi ya sa na ga tashin farko ka bugo Hibban ko? Allah Ya shiryaka Ya Jafar." Fita suka yi falo Uwani ta haɗa musu tea suna cin abinci cikin kulawa da tsantsar soyayya. Suna nan zaune ta miƙa ta buɗe frige ta ɗauko wata jarka da Aunty ta ba ta, ta shanye gabaɗaya kamar yadda Aunty ta faɗa mata, komawa ta yi har za ta zauna ta sake jin motsin Hibban. Gyara masa kwanciya ta yi sannan ta dawo suka ci gaba da cin abinci. Bayan sun gama cin abinci wanka Uwani ta tsala ta feshe jikinta da turarruruka masu ƙamshi, lokacin da Jafar ya fito daga wanka tana gaban mirror. Ta baya ya riƙo ta a hankali ya fara yi mata raɗa a kunne, da sauri Uwani ta ɗago tana zaro ido cikin wasa jin irin kalaman da yake furta mata tamkar ba Jafar ɗinta. Dariya suka saki lokaci ɗaya, ya ja hannunta suka wuce makwancinsu. Mabambamtan saƙwanni Jafar ya shiga aika mata, a wannan karon Uwani ta fitar da kunyarta ta nuna wa mai gidanta tsantsar kulawa da irin kewar da ta yi masa. Hakan ne ya sake birkita Jafar yana ci gaba da nuna mata soyayya, Uwani ta ji daɗi sosai da ta sake fahimtar yadda mijinta yake so da ƙaunarta. Ta shiga narkewa tana shagwaɓe masa shi kuma sai riritata yake yi, daren ranar haka ya zo musu da farinciki musamman Jafar da yake jin wannan daren ya zame masa ɗaya tamkar da dubu. A ranar da Uwani ta koma gidanta bayan da Daddy ya koma gida, suna zauna shi da Aunty suna hira yake sanar da ita a washegari Mami za ta dawo. Aunty ta ji daɗi sosai don haka ta shiga yi musu addu'a da fatan zaman lafiya mai ɗorewa. A take ya kira Mami ya ce mata ta shirya zai zo a gobe ya tafi da ita, saboda farinciki ranar ko baccin kirki Mami ba ta yi ba. Kamar yadda ya faɗa a washegari bayan ya sauke Dada a gida ya wuce ya ɗauko Mami, sai sakin murmushi take yi ga wani irin nauyin Daddy da take ji. Ko da suka koma gida Aunty ta gama girki, duka suka baje a ɗakin Daddy suna cin abinci suna hira. Bayan an gama hira Aunty ta miƙe za ta yi musu sai da safe, Mami ta yi murmushi ta ce. "Amma Auntyn yara tun yanzu kya tafi muna hira." "A'a Mamin yara faɗi dai gaskiya, ina zan zauna na hana amare sakat kina ga Daddyn yara tun ɗazu sai satar kallonki yake. Ai gara dai na ba ku wuri tun Ango bai sallame ni ba."Aunty ta ƙarasa maganar cikin dariyar shakiyanci. "Sharrin da za ki yi mana kenan?" Daddy ya furta yana murmushi." "Ina fa sharri duba fa Daddy ka ga yadda ka kanainaye Mami, wallahi kada idanuna su ƙone bari na yi gaba." Aunty ta yi maganar tana nufar hanyar fita tana dariya. "Wallahi ina nan zan rama Auntyn yara." Mami ta faɗa, da sauri Aunty ta dawo ta ce. "Yawwa na manta Daddy na baka sati biyu cif ka gama cin amarcinka a toh kada ka dawo ɓanagrena kana leƙen sarautar mata kana haɗiyar yawu." Ganin Daddy ya taso da sauri ya nufo wurin Aunty ya sa ta fita da gudu tana dariya. Tura ƙofar Daddy ya yi ya koma kusa da Mami ya janyota jikinsa. "Kwana da kwanaki na yi kewarki." Daddy ya raɗa mata a kunne, Mami ta zuba masa ido tana kallo. Tsohuwar soyayyar shekara sama da talatin da takwas da dawo mata. "Tabbas samun nagartacce kuma ingarman miji kamar kai ba duk maza ba, shi ya sa nake tsananin so da kishinka. Amma na tabbata addu'a ba ta faɗuwa ƙasa banza tun da ta saita zazzafan baƙin kishin da nake da shi a kanka." Mami ta raya a ranta. Ganin ta yi shiru ya sa Daddy ya hura mata iska a fuska. A shagwaɓe Mami ta ce. "Bayan yanzu ka daina sona?" Zaro ido waje Daddy ya yi ya ce, "Wa ya gaya miki, ai ba a ƙin mutum sai dai a ƙi halinsa. Ballatana na rasa wa zan daina so sai Saratuna? Ke ce sarauniyar mata domin soyayyar da nake yi miki ta dabance, ba za ki gane ba amma wallahi na yi matuƙar kewarki a zuciyata." Mami ta ji daɗi sosai da yadda Daddy ya nuna mata kulawa, don haka ita ma ta shiga furta masa kalamai masu tausasa zuciya. Su Jafar ba ƙaramin farincikin dawowar Mami suka ji ba, Mami ta kwantar da kanta suna zama lafiya da Aunty sosai. Haka ita ma Madina ganin mahaifiyarta ta watsar da makamanta ita ma ta sauke take ba wa Aunty girmanta, sai dai shaƙuwar da suka yi ba kamar Auta ba. Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya har Hibban ya kai wata shida, a lokacin ya yi wayo sosai kamanninsa da na mahaifinsa sun sake fitowa. Watarana da daddare Uwani na kwance a cinyar Jafar suna hira ta tashi zaune cikin kulawa ta furta. "Don Allah Ya Jafar ka dawo da Aunty Safna." Lokaci ɗaya ya haɗe fuska, a daƙile ya ce. "Kin daina ƙaunata kenan?" Girgiza masa kai ta yi tana jin zuciyarta na bugawa, don idan ta ce ba ta jin kishinsa ta yi ƙarya. "Na san kina son Jafar kuma kina kishinsa, amma hakan ba zai hana na ba ki shawarar da ta dace ba. Uwani ki samu mijinki ki ba shi shawara ya dawo da matarsa, domin matuƙar kika yi haka wallahi kin gama zama da kowacce irin kishiya ce ba ma Safna ba. Na farko shi kansa mijin sai ya jinjina miki da wannan namijin ƙoƙarin da kika yi, sannan kuma ko ba a gabanki ba na tabbata idan ya dawo da ita sai ya faɗa wa matarsa ke ma kin taka muhimmiyar rawa wurin dawowarta cikin gidan, don haka duk abin da take taƙama da shi za ta sauke. Ki danne kishinki ki nusar da mijinki don wallahi a yanzu na tabbata yarinyar nan ta gama gane kuskurenta. Saboda ba na son a dinga yawo da tambarinki, ana cewa saboda ke mijinki ya saki matarsa duk da abin da ta yi ba na hankali ba ne." Uwani ta tuno nasihar da mahaifiyarta ta yi mata a ranar da ta je gaishe ta, numfasawa ta yi ta furta. "Ba haka ba ne Nur, Aunty Safna ta yi laifi. Amma tun da ka ga mahaifanta da ita kanta sun sauke komai, sun zo har gidanku sun ba da haƙuri na tabbata ta gane kuskurenta. Allah ma fa muna yi masa laifi..." Ɗaga mata hannu ya yi fuska a haɗe ya furta. "Dakata! Daga yau ba na buƙatar jin wannan maganar a bakinki, idan kuma ba haka ba ranki zai ɓaci." Shiru Uwani ta yi, ita kanta ba yin kanta ba ne don dai kawai Innarta ta shawarce ta ne. Shi kansa Jafar a wannan lokacin lumshe ido ya yi, yana jin wani abu na fisgarsa akan Safna. Idan har ya ce ba ya ƙaunarta ko babu ɓurɓushin soyayyarta a ransa to tabbas ya yi ƙarya. Safna ta sauya kamar ba ita ba, ba ta da aiki sai zaman ɗaki. Ta rame ta yi duhu sosai, silar haka ne lokaci ɗaya ta wayi gari da ciwon zuciya. Kusan asibiti uku suka kwanta kuma kowanne da ciwo ya ɗauko warkewa sai ya dawo baya, wannan lamarin ya ƙara ɗaga hankalin mahaifanta. Mahaifiyarta na zaune a gefenta ta ɗago da murya a can ciki ta ce. "Mummy don Allah ki kira mini Jafar, domin a yanzu na yanke ƙauna da sake zama da shi. Ina son ganinsa ko da sau ɗaya ne kafin numfashi ya bar gangar jikina." Hawaye ne ya zubo mata, ta yi wani tarin mai haɗe da kakin jini. Mummynta ce ta taimaka mata ta kwanta tana share ƙwalla, sannan Safna ta ci gaba da cewa. "Don Allah ki ce Jafar ya zo mu yi bankwana da shi." Wayarta Mummynta ta ɗauko ta neman lambar Jafar a sanyaye don ko ta kira ba ya ɗagawa. Kamar almara a wannan lokacin ta ji ya ɗauka, muryar Mummy har rawa take suka gaisa. A nan ta zayyana masa halin da Safna ke ciki da asibitin da take kwance. Duk maganar da suke yi Uwani na zaune a gefe, yana shirin magana da sauri Uwani ta karɓi wayar ta yi sallama. Ƙirjin Mummyn Safna sai da ya buga don ta yi tsammanin rashin mutumci Uwani za ta yi mata. Sai da suka gaisa, sannan Uwani ta nemi address ɗin asibitin ta ce za su zo duba Safna. Bayan sun gama wayar da kanta ta matsa wa Jafar ya shirya ba don ya so ba, kai tsaye asibitin suka nufa. Suna zuwa bakin gate Mummyn Safna ta fito ta shiga da su ciki. Tun da Jafar ya tsoma ƙafarsa ɗakin ƙamshin turarensa ya buge ta, idanunwanta suka sauka a kan na shi. Wani irin bugu ƙirjinsa ya yi da ƙarfi, soyayya da tausayin Safna suka taso masa lokaci ɗaya ganin wata irin muguwar ramar da ta yi. Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank shaidar biya ta wannan number 07062062624 Idan littafi ya kammala cmplt 800 ne☺️ #Ummou Aslam Bint Adam🌚 Cike da rashin tsammani Safna ta dasa ƙwayar idonta a kan Jafar, ba ƙaramin kyau ya yi mata ba don ta ga ya yi haske sosai har wata 'yar ƙiba ya yi. Daga bayansa ta hangi Uwani cikin doguwar rigar abaya, hannunta ɗauke da Hibban. Wani abu ta ji ya tokare ta a ƙirji, kishin Jafar da soyayyarsa suka shammace ta. Sunkuyar da kanta ƙasa ta yi wasu zafafan hawaye suka fara gangorawa daga idanunta. Daga Uwani har Jafar ba ƙaramin mamankin kammanin Safna suka yi ba, ta rame sosai ta yi duhu. A sanyaye Jafar ya furta. "Safna ya jikin?" Saukar kalaman Jafar ya yi daidai da bugun zuciyarta, ta shiga maimaita sunanta a saman harshenta tana mamakin yadda Jafar ya iya furta sunanta kai tsaye saɓanin daɗaɗan sunan da yake furta mata a baya. "Aunty Safna ya sauƙin jikin?" Uwani ta furta ita ma a sanyaye. Sai a lokacin Safna ta ɗago fuska ɗauke da hawaye ta amsa. "Jiki da sauƙi." "Allah Ya ƙara afuwa." Suka furta mata cikin haɗin baki. Shiru ɗakin ya ɗauka hakan ya sa Uwani ta juya za ta fita don ta ba su wuri ko akwai abin da za su tattauna. "Jiddah don Allah ki dakata ina son magana da ke." Safna ta yi maganar cikin karyewar zuciya. Dawowa Uwani ta yi ta zauna a kujerar da ta tashi sannan Safna ta ci gaba da cewa. "Don Allah ki yafe mini abin da ya faru, dama na aikata ne bisa kururuwar shaiɗan. Ki yarda da ni, wallahi har ga Allah a lokacin ban san ke matarsa ba ce." Kuka ya ci ƙarfin Safna. "Koda can ma ni ban riƙe ki da komai ba Aunty Safna, ba ni kaɗai ba ma, a dalilin rashin sanin da ba ki yi ba ne ya sa hatta su Dada suka yi miki uzurin haka. Allah Ya yafe mana gabaɗaya." Uwani ta yi maganar tana sake miƙewa ta fita don ba za ta juri ganin irin narkakken kallon da Jafar yake aikawa Safna mai cike da zallar tausasawa ba. "Don Allah ka yafe mini Daddyn Hibban." Jafar ya yi mamakin yadda aka yi Safna ta san sunan little Umar, ajiyar zuciya ya sauke ya ce. "Na yafe miki Safna, Allah Ya yafe mana gabaɗaya." "A yanzu na gama yanke ƙauna da rayuwa, don haka zan nemi wata alfarma a wurinka. Don Allah idan ba na raye ka taimaka ka yi mini takwara a cikin 'ya'yanka idan ka yi mini haka na san har abada ba za ka manta da ni ba. Domin na san a yanzu ka wuce ajina, ka ga kuwa wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa." Ƙirjinta ta ji ya yi mata wani irin nauyi, lokaci ɗaya ta fara kakarin amai. Da sauri Hajiyanta ta ƙarasa bakin gadon ta ɗauko ƙaramin bokiti ganin tana kiciniyar tallafo Safna ya sa Jafar ya yi saurin riƙe mata bokitin, ɗago Safna ta yi ta fara kelaya aman jini. Sai da ta gama sannan mahaifiyarta ta saka tissue ta goge mata baki, jikin Jafar har rawa yake da ya ga halin da Safna take ciki. Sai da Hajiyanta ta kwantar da ita sannan ta fita ta sake kiran Likita, da sauri likitocin suka shigo sauka buƙaci su Jafar da su fita waje. Jafar na fita ya samu Uwani a reception a zaune, ganin sanyin jikinsa da na Hajiyan Safna ya sa ta shiga jera musu tambayoyi. Jafar ne ya yi mata bayani mahaifiyar Safna ban da kuka babu abin da take yi, suna nan tsaye bayan wani lokaci likitocin suka fito. Kusan su ukun da sauri suka tare su da tambaya. "Jikinta ne ya sake dawowa, amma Hajiya tun jiya da kuka zo asibintin nan mun ce miki akwai wani abu da yake damun yarinyar nan, da ya dace a zauna a tattauna da ita don a ji me take buƙata amma har yanzu shiru." Hajiyan Safna cikin kuka ta ce. "Likita abin da Safna take so ne ba za ta samu ba, don haka babu fa'idar sake tattaunawar." "Amma Hajiya wanne irin abu ne haka? Kuma kun taɓa jarrabawa ba ku sama mata shi ba?" Likitan ya tambaya. Hajiyan Safna ta gyaɗa kai tana goge hawaye. "Allah shi ya ba mu Safna ita kaɗai, kuma ina ganin wannan na daga cikin layin ƙaddararta ne. Idan tana da kwana a gaba sai ka ga ta tashi, idan kuma babu haka Allah ya ƙaddara." Shi kansa jikin Likitan ya yi sanyi, ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Idan kin gama ina son ganinki a office." Daga haka ya wuce. Sallama Hajiyan Safna ta yi wa su Jafar sannan ta bi bayan Likitan, jiki a sanyaye suka nufi mota babu mai iya magana a cikinsu. Tabbas so ba ƙarya ba ne, Jafar tuƙi kawai yake amma hankali da zuciyarsa na wurin Safna. Kamar Uwani ta san abin da yake zuciyarsa ta furta. "Nur!" Waigowa ya yi ya kalle ta ba tare da ya amsa ba. "Safna na buƙatar kulawarka! Ya zame maka wajibi ka yi wannan jihadin ko don ceton rayuwarta. Tana cikin mawuyacin halin da duk rashin imanin mutum dole ya tausaya mata, duk wannan ka san mene ne sila?" Ta wurga masa tambaya. Girgiza mata kai ya yi. "So da ƙaunarka sune silar faruwar halin da take ciki, belive me idan har ka ce za ka dawo da ita za ta samu lafiya cikin yardar Ubangiji." Shiru Jafar ya yi ya mayar da kansa titi zuciyarsa na juya maganganun Uwani. Washegari da sassafe Daddy ya kira Jafar a waya yana yi masa faɗa game da halin da Safna take ciki, dalilin wayar da suka yi shi da mahaifin Safna musamman da ya ji irin mawuyacin halin da take ciki. Sun jima suna waya sannan suka yi sallama, shiru Jafar ya yi hakan ya sa Uwani ta tisa maganganun da ta yi masa a game da Safna. Uwani da kanta ta shirya Jafar ta ƙarfafa masa gwiwa ya tafi asibitin. A lokacin da ya je asibitin Hajiyan Safna na ganinsa bayan sun gaisa ta haɗa hannuwa biyu alamar roƙo ta ce. "Mun gode ƙwarai Jafar da kulawar da ka nuna wa Safna, amma don Allah kada ka kuma zuwa wurinta domin ganinka ya jefa ta cikin mawuyancin hali. Ina fatan za ka yi mini kyakkyawar fahimta, domin a kullin ta yi tozali da kai yana tayar mata da mikin da ya haddasa mata lalurar da take ciki." Ta ba shi tausayi matuƙa sai da ya gama sauraronta ya ce. "Mummy na zo ne domin na sanar da Safna zan mayar da ita, In Shaa Allahu jibi Juma'a za a mayar mana da aure..." Tun bai gama magana ba Mummy ta riƙo hannunsa tana tattaɓawa. "Da gaske Jafar kai ne kuma abin da kake faɗa haka ne?" Gyaɗa mata kai ya yi, suna nan jikin ƙofar suka ji motsin Safna. Jafar ne ya shiga tana ganinsa a wannan karon ma kallonsa take tana hawaye. Sai da ya ja kujera ya zauna ya sunkuyar da kansa daidai fuskarta ya sakar mata murmushi sannan ya furta. "Goge hawayenki Cutiena!" Kamar a mafarki ta ji kalaman nasa, take ƙirjinta ya shiga bugawa da sauri. Hannu na rawa ta goge fuskarta, har lokacin kallonsa take murya a sanyaye ta ce. "Ya Allah idan mafarki nake yi kada ka sa na farka a yanzu." "Ba mafarki kike ba Habibty!" Jafar ya faɗa yana sakar mata murmushi. Hannu ta kai ta shafi fuskarsa don ta tabbatar da kokontanta. "Ina farincikin sanar da ke ranar Friday su Daddy za su mayar da aurenmu." Da sauri ta zaro ido waje hakan da ta yi ba ƙaramin birge shi ya yi ba, iska ya hura mata a fuska ya kashe mata ido ɗaya. Kunya ce ta kamata ta yunƙura da ƙyar za ta tashi, Jafar har zai taimaka mata ya tuna a wannan lokacin ba matarsa ba ce. Hajiyanta ya fita ya kira ta zo ta taimaka mata, fita ta sake yi ta ba su wuri. "Amma maman Hibban ta san da haka kuwa? Gani nake kamar ba za ta..." Da sauri Jafar ya katse ta da faɗin. "Jidda ce ta ƙarfafa mini gwiwar da na iso wurinki a safiyar nan cike da ƙwarin gwiwa, Jidda ta dabance a cikin mata domin tana da kyakkyawar mu'amala, sai kun zauna za ki fahimci haka saboda ita mutuniyar kirki ce. Kuma jajirtacciya 'yar aljanna." "Jafar da ko hirar wata 'ya mace bai taɓa yi mini ba amma yau shi ne yake yabon matarsa a gabana, tabbas jiya ba yau ba ce." Safna ta raya a ranta. Murmushin ƙarfin hali ta saki sannan ta ce. "Ko a jiya na fahimci haka." Jafar ya jima a wurin Safna yana janta da hira, hatta ruwan tea shi ya ba ta da kansa. Sai kusan Azahar sannan ya bar asibitin. Likitan da ke duba Safna ba ƙaramin mamakin sauyin da aka samu ya yi ba, shi kansa Daddy ya ji daɗin ganin yadda ya je ya same ta a zaune har suka yi hira. Kuma tun daga ranar jikin Safna ƙara gaba yake yana yin kyau, saboda kullin sai Jafar ya je asibitin sun yi hira ya ɗebe mata kewa. Ranar Juma'a bayan sallar Juma'a ne aka mayar da auren Safna da Jafar a masallacin Juma'a na Rjiyar Zaki, mahaifin Safna ban da godiya babu abin da yake yi wa Daddy. Ita kanta Mami ta sauko don da farko cewa ta yi ba ta lamince Jafar ya dawo da Safna ba, sai da Daddy ya yi mata nasiha sannan ta amince. Uwani ta dage sosai da sallar dare tana addu'ar Allah ya yaye mata zafin kishin da take da shi, don ta san abu ne da sai ta kai zuciya nesa kafin ta saba da shi. Cikin abin da bai fi sati uku ba tuni Safna ta warke garau, jikinta har ya fara dawowa duk da dama can ita ba mai jiki ba ce. Kuma saboda yanayin rashin ƙwarin jikinta Daddynta ya ce sai bayan ta warware za ta tare. Jafar kusan kullin sai ya leƙa gidansu Safna ya duba jikinta, duk taku da sauyin Jafar Uwani na lura da shi sai dai ko a fuska ba ta taɓa nuna masa komai ba. A satin da Safna za ta koma ne aka yi mata gyare-gyare a ɓangarenta, ita ma Uwani Jafar ya sauya mata abin da yake da hali har da ɓangaren suturu duk da tana da wadatattu. "Uwar biyu wallahi duk wata addu'a da na sani babu wacce ba na yi amma har gobe babu abin da ya ragu a zuciyata. Ina son Ya Jafar ina matuƙar kishinsa, ban san son shi ya kai haka a zuciyata ba sai da na ji tariyar Aunty Safna." Uwani ta ƙarasa maganar ƙwalla na zuba. Auta da ke zaune da tsohon ciki ta sauke ajiyar zuciya ta ce. "Tun farko ke ce ba ki yi shawara da ni ba, matar da ta so halaka ki ita ce kike son a kwaso a dawo miki da ita kusa da ke. Yanzu dai tun da aikin gama ya gama shi kenan, addu'ar dai za ki ci gaba, ina da wasu addu'o'in zan turo miki ta Whatsapp In Shaa Allah." "Idan ma ban ba shi shawarar dawo da ita ba Auta ban san nan gaba wacce Ya Jafar zai kawo mini ba, domin duk son da namiji yake yi maka ɗari bisa ɗari ba za ka ce da kai kaɗai zai zauna a rayuwar duniya ba. Kuma ko ke shaida ce Safna da iyayenta sun matuar gane kuskurensu." Uwani ta furta a sanyaye. Auta ta jinjina kai, sannan ta cigaba da kwantar wa da Uwani hankali har ta ji damuwar da ke ranta ta yaye. Bayan sallar Isha'i suna zaune suka ji motoci na shigowa, Auta ta dafa Uwani da idanunta suka ciko da ƙwalla ta ce. "Don Allah kada ki ba ni kunya." Jinjina kai Uwani ta yi ta haɗiyi yawu mai ɗaci. Suna nan zaune suka ji an nufo sashenta, wasu dattawa biyu ne riƙe da Safna. Cikin karamci su Uwani suka karɓe su bayan sun gaisa suka wuce da Safna sashenta. Sai da duka mutanen da suka rako Safna suka watse sannan Jafar ya shigo gidan, kai tsaye sashen Uwani ya wuce Auta na ganinsa ta ce. "Ya Jafar wai ina ka maƙale tun ɗazu fa Dr ke jirana." "Ai mun gaisa da shi a bakin gate, zo ki wuce ku tafi gida." Jafar ya furta yana zama a kusa da Uwani. Da ƙyar Auta ta yunƙura ta miƙe, sai da ta yafa mayafi sannan ya ɗauki jakarta ta ja hannun Uwani suka wuce uwar ɗaki. "Ke fa dama munafuka ce me za ki kitsa wa matata?" Jafar ya faɗa ganin sun shige ɗaki. "Ya Jafar saƙo za ta ɗauko mini." Auta ta faɗa tana turo ƙofar. "Maman Hibban don Allah yanda kika yi jarumta ki ci gaba, trust me za ki ce na faɗa miki a nan gaba za ki yi alfahari da wannan ƙoƙarin naki. Ki fa tsare gida kin san ke ce babba kar ki sake ki yarda girmanki, kuma ko da wasa kar ki ɗauki raini, atoh don wallahi duk a yadda ta zo miki ku tafi a haka na san ki sarai 'Yar ƙashin gwiwa ban da case a nan fannin." Uwani da Auta suka saka dariya, Auta ta jima tana tausar Uwani sannan suka fito ta yi mata rakiya. Sashenta ta koma ba ta samu Jafar a falo ba, ta zauna babu jimawa suka shiga shi da Safna. A mutumce Safna ta gaida Uwani, ita ma ta amsa mata fuska a sake har Uwani na zolayarta. Nasiha Jafar ya yi musu sosai kowacce ya nuna mata matsayinta, bayan ya gama Uwani ta lura da yadda Jafar yake jin nauyin ya ce Safna ta tashi su wuce sashenta. "Ango dare fa yanayi, kaga akwai gajiyar taro amarya na buƙatar hutawa." A sanyaye Jafar ya kalle ta, sai a lokacin ya sake lura da 'yar ramar da ta yi. Miƙewa Jafar ya yi ya nufi hanyar fita Safna ta bi shi a baya. Suna fita Uwani ta jingina da ƙofar ta sauke ajiyar zuciya tana jin zuciyarta na zafi, motsin Hibban ta ji a ɗakinta da sauri ta ƙarasa wurinsa. Sai da ta gama ba wa Hibban ya sha ya koma bacci sannan ta faɗa toilet ta watsa ruwa, ta saka rigar bacci tana fitowa Falo ta ga Jafar a zaune. "Me ya dawo da kai kuma?" Uwani ta furta tana ɗan zaro ido waje. Hannu ya buɗe mata yana murmushi, maƙale kafaɗa Uwani ta yi ta nuna masa ƙofa da hannunta. "Aunty Safna na can tana jiranka fa!" Tasowa ya yi ta matsa gabanta, rungumo ta ya yi ta shiga kiciniyar zillewa. "Ya Jafar..." Kalamanta suka katse sakamakon mayar mata da su da ya yi da bakinsa cikin bakinta. Da ƙyar ta samu ta ɗago Jafar ya marairaice murya ya ce, "Jiddah yau kora ta kike yi?" "Saboda lokacin amarya ne! Wallahi ba za ka zo ka birkita ka tafi..." Shiru ya yi yana kallonta, tausayinta yake ji don ya san wace ce ita da irin zafin kishinta. Amma ta yi matuƙar birge shi ganin yadda take iya sarrafa kishin nata. "Jidda kin fitsare idonki a gabana kike faɗar zan yamutsa ki?" Hijabinta ta janyo ta zura ta ja hannunsa tana faɗin. "Wallahi dare na yi ba za ka bar mana amarya ita kaɗai ba." Har sashen Safna ta kai shi a bakin ƙofa ta tsaya ta ce. "Sai da safe Nur!" Ta furta a sanyaye. Janyota ya yi ta faɗo jikinsa ya bi gefen kunenta ya furta. "Allah Ya yi miki albarka Jiddah, ina ji a jikina ke 'yar Aljannah ce. I always love you." Ya yi maganar yana sakar mata fake a goshi. Idanunta suka ciko da ƙwallah jin wani irin kishi da soyayyarsa na taso mata. "I love you too Nur." Ta furta, har ta fara tafiya Jafar ya riƙe hannunta yace zai yi mata rakiya. Sai da ya sake raka ta bakin ƙofa ya dawo yana jin zuciyarsa wani iri. A gurguje Uwani ta shiga cikin ɗakinta ta faɗa kan gado ta fashe da wani irin kuka mai cin zuciya. Sai da ta yi mai isarta sannan ta je ta ɗauro alwala ta fara gabatar da sallah, ta jima tana kai kukanta wurin Ubangiji bayan ta gama ta koma gado tana lazumi a haka bacci ya yi awon gaba da ita. Lokacin da Jafar ya shiga Safna har lokacin na zaune a wurin da ya bar ta, sauke mata mayafin jikinta ya yi yana lakutar hancinta. Murmushi ta saki, ya ja hannunta suka ɗauro alwala bayan idar da sallar suka zauna suna cin kazar amarci. A kunyace Safna take ci har suka gama, sannan Jafar ya fara aika mata da saƙwannin soyayya. Ya yi mamakin irin nauyinsa da Safna take ji, Safna ba ƙaramin daɗi ta ji ba ganin yadda Jafar ya nuna mata kulawa da soyayya. Hakan ne ya sa ta samu ƙwarin gwiwar mayar masa da martani. Washgari tun asuba Uwani ba ta koma bacci ba, ita ta haɗa musu kayan breakfast. Nata ta ɗora a kan dianing ta ajiye, na su Jafar ta saka musu a basket ta ajiya. Sai da ta zo gyaran falo ta tuna da kazar da Jafar ya ba ta, kitchen ta kai sannan ta shiga wanka bayan ta gama shirya Hibban. Shiryawa ta yi cikin doguwar rigar jar atamfa, ɗinkin ya mata kyau sai dai fuskarta ta yi fayau. Ta fito falo kenan ta ji shigowar Safna da Jafar, tana ganinsu ta ji wani abu ya tokare ƙirjinta. "Innalillahi wa inna'ilahir raji'un." Ta furta don ta ji sanyi a ranta. Ta ƙarasa fuska ɗauke da fara'a ta tarbe su, sai da suka gaisa ta miƙa musu abincin breakfast. A kan dianning Jafar ya ɗora ya shiga zuba musu don ya ce a nan za su ci tare. Safna ba ta saki jikinta ba, don yanayin yadda Jafar ke kallon Uwani yana janta da hira ne ya ɗan sosa mata zuciya, sai da suka gama sannan suka koma sashesu. A haka kwanaki suka ci gaba da tafiya kullin Uwani ke yi musu girki har tsawon kwana ukun da musulunci ya wajabta ga bazawara, sannan suka fara rabon kwana bibbiyu a tsakaninsu. Da farko zaman Safna da Uwani lafiya ƙalau suke yi kowa yana takatsantsan wurin shiga haƙƙin ɗan uwansa, daga baya sai zaman ya fara sauya salo musamman idan Jafar yana ɗakin Uwani. Duk ranar girkin Uwani sai Safna ta tsiri rashin lafiya ko ta ce tsoratata ake yi tana jin tsoro, musamman da a wannan lokacin Uwani ta lura kamar Safna na da ƙaramin ciki. Sau tari idan Safna ta yi haka sai dai Jafar ya tafi sashenta don ya taya ta kwana, wani lokacin kuma cikin dare za ta yi masa waya ta saka kukan wai tana jin tsoro. Tun abin ba ya damun Uwani har ta lura abin kissa ce ga shi idan ta yi magana sai Jafar ya fara faɗan ba a son barin mai ciki cikin damuwa. Wannan ya sa Uwani ta fara wata irin rama a tsaye, ganin abin ba na ƙare ba me ya sa ta ƙudurta a ranta za ta ƙwatarwa kanta 'yanci a cikin ruwan sanyi. Kamar yadda Safna ta saba, Uwani da Jafar suna kwance wayar Jafar ta fara ringing. A hankali Jafar ya janye hannunsa daga jikin Uwani, sai da ya ja blanket ya rufe jikinsa sannan ya ɗauki wayar. Takaici goma da ashirin ya lulluɓe Uwani, saboda ɓacin rai miƙewa ta yi ta janye blanket ɗin jikinta. Towel ta ɗaura sannan ta faɗa toilet ta tsarkake jikinta, doguwar rigarta ta saka ta koma kan stool ta zauna tana sauraron Safna da ke faɗin. "Baby wallahi tsoro nake ji sai na ji kamar ana tafiya, ga shi yanzu haka cikina wani irin ciwo yake yi." Safna ta ƙarasa maganar tana shasshekar kukan ƙarya. Jin haka ne ya sake rikita Jafar a gaggauce ya ce. "Gani nan zuwa bari na zo." Kashe wayar ya yi ya faɗa toilet sai da ya yi wanka sannan ya zura jallabiyya yana shirin fita Uwani ta miƙe ta ce. "Bari na raka ka Ya Jafar don ni ma fa da rana sau biyu na ga ana giftawa, ko kuma na ji ana kiran sunana. Gaskiya ina zargin gidan nan akwai motsi a cikinsa." Tare suka fita Jafar sai zuba sauri yake, suna gab da fita saga sashenta Uwani ta dafe kai tana faɗin. "Wash kaina ya sara mini Ya Jafar, kamar an buga mini guduma." Riƙo ta ya yi yana mata sannu, za ta yi kusan sakan ashirin dafe da kai sannan ta ɗago suka ci gaba da tafiya. Uwani kallon Jafar ta yi sai kawai ta zaro masa ido haɗe da kyalkyalewa da dariya. Mamaki ne ya kama Jafar ganin abin da Uwani take yi, cikin ƙarfin hali ya basar kamar bai ganta ba. Suna gab da shiga sashen Safna Uwani ta cafko hannu Jafar tana ƙyaƙyata dariya ta ce. "Matar Tummo." Da sauri Jafar ya waiga suna haɗa ido da Uwani ta gwalo masa idanu tana ta sake cewa. "Matar Tummo" Jikin Jafar ne ya fara rawa, a hankali ya fara son ƙwace hannunsa Uwani ta riƙe shi ƙam. A ransa yana maimata sunan matar Tummo. A haka suka ƙarasa sashen Safna, Safna a tunaninta Jafar ne don haka tana zaune daga ita sai wani ɗan matsattsan three quater wando. Ganin Uwani ya sa ta yi turus tana haɗe fuska, Jafar na shirin tambayar Safna jikin nata suka ga Uwani ta buga wata uwar sufa ta nufi kan dianning ɗin Safna, da sauri ta fisgo gwangwanin madara ta cire murfin ta ɗaga kai tana zazzaga garin madarar a bakinta har zuwa fuskarta. Sai kuma ta waigo wurin Jafar ta wani zare ido ta ce. "Yar bugus uwar 'yan iskan aljanun zamani zo kin ga mijinki can wanda ya koma ɗan shafi mu lera." Uwani ta gama maganar tana yin wurin su Jafar da gudu, a guje Jafar da Safna suka matsa Uwani ta gimtse dariyarta ta maƙale murya ta ce. "Ki bar Ɗan Tummo wallahi zan biyo shi sai na mayar da bakinsa ƙeya." "Jidda lafiya mai yake faruwa?" Jafar ya faɗa yana daga ƙarƙashin dianing. Watso masa manyan idaunta ta yi ta ce. "Kai ne mijin Yar bugus da ka ɓata wa 'Yar autar mai martaba rai." A razane Jafar ya ce. "Waye 'yar bugus da mijinta kuma? Ni kamar yaya?" Uwani ta fakaici Safna ta buga wata uwar sufa ta fusgo gajeren wandonta, nan take silla-sillan siraran mazaunan Safna masu kama da sandar ba'are suka bayyana, Uwani da Safna suka hau kiciniya kowacce tana fusgar gajeren wandon. Cikin tashin hankali Safna ta fasa ihu tana faɗin. "Baby ka taimaka mini don Allah, wallahi za ta yi mini tumɓur." Jafar da ya ja kwanuka ya sake rufe kansa da su plates ya ce. "Wallahi ba zan iya ba lamarin nan ya fi ƙarfina Dear." "Ba dai so kike ki hana 'yar autar mai martaba jin daɗin zaman aure ita da mijinta ba? Wallahi kema sai mun haɗa ki da mijin 'Yar bugus ya shafe miki hallitun jikinki sai mu ga ta faɗin makirci." Uwani ta faɗa tana zuba wa Safna duka a cinya da mazaunanta. Hawaye shaɓe-shaɓe a fuskar Safna ta ce. "Don Allah ku yi mini rai kada ku shafe mini hallituna." Uwani ba ta bi ta kan Safna ba ta waiga wurin Jafar da ke ta haɗa gumi ta gwalo masa ido waje tana zaro harshe ta ce. "Kai ma so kake ka zama marar adalci ko? Wannan munafukar matar taka babu abin da yake damunta amma kullin sai ta yi ƙaryar ana tsoratata ko ba ta lafiya da dare. Wallahi kai ma babu abin da zai hana ba mu shafe hallitunka ba, ko kuma a yanzu mu mayar maka da hallitar matarka jikinka ita kuma mu mayar mata da naka. Kai idan har muka ji daga bakin 'Yar auta ko mata-maza take so tsaf za mu mayar da kai." Hankalin Jafar ba ƙaramin tashi ya yi ba, musamman da ya tuna abin da ya faru da Lado a kan awakin Uwani. Da sauri Jafar ya kai hannu ya fara shafa ƙirjinsa sai da ya ji shi a daidai yake, sannan ya sauke ajiyar zuciya ya ce. "Don Allah ku faɗi abin da kuke so idan laifi ne muka yi muku ba za mu kuma ba." "Mu ba za mu faɗa ba sai dai matarka ta faɗa da bakinta, ke munafuka ki faɗa da bakinki shin mu jinsin Aljanu mun taɓa tsorata ki, ko kuma akwai wani ciwo da yake damunki ban da makirci irin naku na mata?" Safna ta share ƙwalla jiki na rawa ta shiga wassafa duk irin ƙarairayin da take yi, sannan ta ɗora da cewa. "Don Allah ku gafarce ni wallahi ba laifina ba ne har da zugar ƙawaye, sune suka ɗora ni a wannan turbar." Daga Jafar har Safna ban da haƙuri babu abin da suke ba wa Uwani, Uwani ta ɗauke kai gefe tana gimtse dariyarta ta ce. "Wallahi kun ci sa'a 'Yar autar Mai martaba na da sauƙin kai, kuma Ɗan Tummo sabon ɗan shafi mu leran cikin jinsinmu ba ya nan, za mu ɗaga ƙafa domin mu gani idan da gaske kike kin yi nadama. Kai ma kuma za mu ci gaba da bibiyarka, idan ka sake yin rashin adalci wallahi sai mun shafe hallitarka ta koma kamar bayan babe." Uwani na gama faɗar haka ta saki jiki ta faɗi ƙasa yaraf, irin faɗuwar da ta yi duk wanda yake wurin ba zai taɓa tsammanin aljanun ƙarya ta yi ba. Ita kanta ta bugu sosai, amma ganin yadda daga Jafar har Safna suka tsorata ta san ba za su sake yi mata iskancin da suke yi mata ba. Atishawar ƙarya Uwani ta fara jerawa, a daidai lokacin Jafar ya ƙarasa ya taimaka mata, sai dai har lokacin ta lura a tsorace yake. "Ya Jafar mene ne wannan kamar madara a jikina?" Uwani ta tambaya kamar ba ta san komai ba. "Ni na zo ɗauko madara zan haɗa wa Safna tea madarar ta ɓare ta zubo miki a jiki. Ta so maza mu koma sashenki ai jikin nata da sauƙi ta samu lafiya." Uwani ta saci kallon gefen wurin da Safna ke zauna, ta ga ta yi zumu-zumu ta saki murmushi a fakaice cikin ranta Uwani ta furta. "'Yar iskar ƙarya da ni za ku dinga yi wa iya shege, Allah ya taimake ku ba bulala na sa na zane ku ba." Tun da Uwani ta yi wa Safna haka shi kenan ta samu 'yanci ranar kwananta, a ɓangare ɗaya kuma shakkar Uwani ta mamaye ta. Daga ƙarshe ma sai Safna ta watsar da komai, suka cigaba da zama lafiya da kwanciyar hankali. Tammat Bi HamduLillah A nan labarin UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA ya zo ƙarshe. Kuskuren da yake ciki Allah Ya yafe mana, darussan da ke ciki Ubangiji ya ba mu ikon ɗauka. A kullum ina faɗa muku ni ma 'Yar adam ce tara nake ban cika goma ba, idan an ga kuskure a yafe mini. Kuma ina fatan Ubangiji Ya yafe mana bakiɗaya.👏🏻 Mu tara a cikin ci gaban littafin SHU'UMAR MASARAUTA 2 ku kuma haɗo da addu'ar Allah ya sa na juri typing ɗinsa😂 ga dai labarin da komai na gama tsarawa sai dai typing ɗinsa kamar an saka mini hannu. Ina yi muku fatan alheri da godiya musamman waɗanda suka fitar da kuɗinsu suka sayi littafina, Allah Ya saka da alheri Ubangiji Ya bar zumunci. Idan akwai ƙorafi a game da labarin Uwani ina sauraro, kuma a shirye nake na bada amsoshin a kan kowacce tambaya. Littafin kuɗi ne 500 ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank shaidar biya ta wannan no 07062062624 Littafi ya kammala cmplt doc 800 ne. #Ummou Aslam Bint Adam🌚