[31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ __________ *BOOK2* _______________*PAGE1* _____Jabir bai kai da cika burin sa a kan Amra ba, Allah ya koro wani bawan Allah da ke nan maƙota ya fito zai je masallaci, Kawai ya hangi aika-aikan da Jabir yake shirin aikata wa, Shi yasa ya isa wurin yana dalle su da tocila tare da faɗin, "wane ne a nan? Kai! Kai! Lafiya? Me kake shirin aikata wa haka?" Take Jabir ya dawo hayyacinsa yana kallon mutumin cikin wani irin yanayi "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Là haula fisha'atil lah, kar dai a ce fyaɗe zaka yi mata?" Cikin ƙarfi yayi furucin yana ƙara dalle shi da tocilan hannunsa, take kuma ya soma waige-waige yana neman ko zai ga mutane, ganin babu kowa sai ya soma ihun kwarto yana faɗin, "jama'a don Allah ku taimaka mana ga kwarto." Ai Jabir na jin haka ya ɗaga Amra yana riƙe da wandon sa da ya cire mazugin, take ya watsa a guje ƙafa mai na ci ban baka ba "Ka ji min matsiyacin Yaro, amma kam an yi asarar haihuwa a nan, ya rasa wacce zai afka ma wa sai kanwarsa? wannan ai Amra ce ta gidan Malam Garba." Ya ƙare maganar yana sake haska ta, ganin bata numfashi alamun ta sume ne, Shi yasa ya gyara mata doguwar riganta ya cicciɓe ta tunda duk ihun nan da yayi babu wanda ya ji sa, take ya ɗauke ta zuwa cikin gidan su yana kwaɗa sallama Mama da hankalin ta ya tashi saboda jin shiru har yanzu Amra bata dawo ba, duk sun kasa sukuni daga ita har su Afra, suna zaune a ɗaki sun yi jigum Afra tana furta, "Mama ko in bi bayanta ne in gani? Kinga fa lokacin shigowar ta yayi amma shiru, ga shi har an kira sallah ana gab da shiga." Mama bata kai ga yin magana ba suka ji sallaman maƙocin su wanda tuni sun shaida muryansa, Malam Aƙilu ne, Shiyasa Mama ta amsa mishi tana miƙe wa tare da ƙara faɗin, "ana zuwa Malam Aƙilu." Da fitan ta sai ta ga ya ɗauko Amra a hannunsa, take gabanta ya faɗi ras; cikin sauri tace, "Malam kamar Amra nake gani a hannunka?" "Ƙwarai kuwa ita ce, taimaka min in ajiye ta." Yayi furucin yana sake nufo inda take Ita kuma jiki na rawa ta buɗe mishi labulen ɗakin tana cewa, "ka shiga da ita ciki." Ɗakin ya kaita ya shimfiɗe ta a kan gadon Mama Inda su Afra tuni sun tashi tsaye suna kallon ikon Allah ganin yanda aka shigo da Amran, ko Hijabi babu a jikinta, rigan jikinta ma a yage; gashin kanta duk ya barbaje, babu inda jikinsu ba ya rawa musamman ma Mama, ganin kamar ba ta nimfashi lokaci guda hankalin su ya ƙara tashi Mama cikin tsananin ruɗe wa take faɗin, "don Allah Malam Aƙilu mai ya samu ƴata ku ka shigo a haka? Wani abun ne ya same ta? Faɗa min don Allah kar zuciyata ta fashe?" "Wlh Allah ne ya taimake Ni nima na fito daga gida, na ga wannan Yaron ɗan wurin Babansu, wato Jabir kenan, yana ƙoƙarin aikata mata alfasha, ita yarinyar har ta sume ma, to zuwan nawa ne ma yasa ya gudu wlh, amma da tuni ya ida nufin sa a kanta." "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!" Take Mama ta fashe da kuka tana sake rafka salati cikin tsananin ruɗu da tashin hankali, babu inda jikinta ba ya rawa sabida jin abun da Malam Akilu ya faɗa "Sai dai haƙuri, amma ku ɗauki mataki sabida kar wannan matsalar ta ci gaba da afkuwa, kun san yaron nan ba hankali ya cika ba sabida shaye-shayen da yake yi, ku killace Yaranku ku dena barin su suna fita sakaka, Allah ya tsare gaba, bari in fita in kwaso mata sauran kayan ta da yake wurin." Mama na kuka take mishi godiya duk ta rasa abun faɗa Sai yace, "babu komai, bari in je." Ya fita ya bar su a nan cirko-cirko daga Maman har su Afra kuka suke yi "Mama don Allah ki ɗauki mataki kar ya ci galaba a kan Aunty Amra, don Allah kar ya kashe mana ita." Afra tafada hakan tana fashe wa da wani sabon kukan mai cin rai "To ya zan yi Afra? Jabir bai da hankali bai da tunani, kina ganin yanda nake suntiri wurin Ubansa amma ƙarshe reshe ne ya juye da mujiya, cewa yayi ma in har na sake tako ƙafana gidan sa ya rantse da Allah sai ya amshe ku kun koma wurin sa, kuma hukuma zata raba mu, mu da zamu kai ƙaran sa shine zai kaimu ƙara tunda bamu da Fawan da za a dube mu." Ta ƙare maganar tana share hawaye da gefen zani, yayinda takai duba ga inda Amra ke kwance Malam Aƙilu ne ya shigo gidan yana sake sallama Mama fita tayi ta amshi kayan tana sake mishi godiya kamar zata duƙa mishi Shi kuma yana jaddada mata, "ta dauki mataki tun kan ya kaita ya baro ta, sannan ta dena barin su suna fita ko kofar gidan ne da zaran yamma tayi gudun samun matsala." "To Malam, Nagode sosai, Allah ya saka." "Babu komai, sai da safen ku." Ya juya ya fita a gidan Ita kuma bakin ƙofan ta nufa ta rufe gidan sannan ta dawo ta shiga dakin, Su Salma duk sun kewaye Amran suna kallonta, Mama tace ma Salma, "ta ɗibo mata ruwa ta zuba mata su gani ko zata farfaɗo." Ruwan ta kawo, Mama ta amsa ta zuba mata tana ta shafa mata a kan fuska Can kuwa sai ga shi ta ja dogon numfashi ta soma motsi, tana buɗe idanunta kuwa ta saka ƙara mai firgitar wa, wanda ya tsorata su dukka, Da alamu a firgice take sai ihu take yi tana ƙoƙarin tashi ta gudu Amma sai Mama ta danne ta tana kiran sunan ta cikin tashin hankali, "Amra ki natsu, mu ne tare da ke, don Allah ki natsu." But ina ba ta jin ta, a yanda take ihu da rawan baki jikinta sai kerma yake yi, gaba ɗaya ta tsorata ta firgice don gani take yi kamar har yanzu tana wurin Jabir ne yana aikata mugun nufin sa, tayi mugun fita a hayyacinta bata san ma wa ke kanta ba Sai hakan ya tayar wa su Afra hankali, suma suka saka kukan hankalinsu a tashe suna kiran sunan ta Ɗakyar Mama ta danne ta tana mata addu'a zuciyarta cike da damuwa da tausayin ƴarta Sai daga baya ne Amra ta soma dawowa cikin hayyacinta ta gane tana tare da su Mama ne, hakan ne yasa ta rungume Maman ƙam; nan take ta sake fashewa da wani irin kuka mai cin rai da ɗacin zuciya, babu inda jikinta ba ya rawa Mama kuma hannu tasa a kanta tana shafa ta ranta babu dad'i, "ki yi shiru don Allah haka nan Amra kar ki ja wa kanki wani ciwon, babu abinda zai faru da ke Insha Allahu, Allah ke tsare wa kuma shi zai tsare ki da ikon sa, babu wani mugun da zai ida nufin shi a kanki, Insha Allahu sai Jabir ya ga ƙarshen shi bazai taɓa cin nasara a kanki ba." Sai kuma ga hawaye ya zubo mata sharr; yayinda take jin zuciyarta na tafarfasa tana jin ɗaci daga ƙasan ranta Ɗago da kanta Amra tayi tana kallon Maman idanunta jazur har sun kumbura sai fitar da ruwan hawaye suke yi, nan ta soma mata bayani jikinta sai rawa yake, burin ta kawai ta sanar mata da abun da ya wakana, ɗakyar take iya sarrafa hannun nata ma sabida tashin hankalin da take ciki, ba kaɗan ba ta tsorata lokaci guda ta fita a hayyacinta sai ɓarin jiki take yi tana haɗiyar yawu Hannu Mama ta sanya ta sauke nata hannayen tana cewa, "na ji bayanin komai a wurin Malam Aƙilu, ke ce ma ba kya jin magana Amra, sai da na faɗa miki ki dena kaiwa dare wannan ba maslaha bane, to ga shi kin je kin ja wa kanki ya biyo ki a wannan lokacin, da ba don Allah ya kawo Malam Aƙilu ba da tuni ya cutar da ke, daga yau kar in sake ganin kin kai dare irin haka, da zaran an sallame ki ki dawo gida, idan muna tare babu yadda za a yi ya cutar min da ke, da iya karfina zan kare ki bai isa ya ci galaba a kanki ba, bani da yanda zan yi ne, da akwai dole zamu bar gidan nan ko don in tsiran muku da mutuncin ku, Allah ne gatan mu insha Allah sai Allah yayi mana maganin sa, kuma daga yau zan ɗauki mummunar mataki a kansa wlh, gidan nan ma bazai sake shigo shi ba." Haka Mama ta dinga faɗa ranta duk a ɓace sabida baƙin cikin abin da Jabir yake musu Yayinda Amra kuwa kanta ta ɗaura a kafaɗan Mama tana ta sauke ajiyar zuciya, har a lokacin a tsorace take, ta ƙanƙame ta ƙam tana kerman jiki Duk yanda Mama ta so ta kwantar wa da Amra hankali, amma inaa hakan ya faskara, domin ba ƙaramin tsorata tayi ba, abu kaɗan sai ta firgita kamar ta ga abin tsoro, ta ƙanƙame ta ƙam ta ƙi barin ta ta matsa, dama tana da tsoro kuma ga shi Jabir ya ƙara dasa mata tsoron sa Ita kanta Maman a dame take, haka suma su Afra ganin yanda ƴar uwansu take cikin wani hali, Ɗakyar Mama ta lallaɓa ta tayi sallah, shima sai da taimakon Afra don ita ta raka ta bayin, ita kuma Mama da Salma suna bakin ƙofan suna jiran su, Sai da suka yi alwala dukkan su sannan suka koma ɗakin ta, ƙarshe ma a ɗakin suka ci abinci tace, "su hau gadon ta su kwanta gaba dayansu." Bayan sun yi Sallan isha'i, A tsakiya suka saka Amra ta manne da jikin Afra Ita kuma Mama tana zaune tana kallon su cikin tsananin damuwa da tunanin mafita, tana ji a ranta anya baza su siyar da gidan nan su canza wuri ba? Koda gidan da bai kai wannan bane sai su siya sauran kuɗin ta ɗaura jari, amma ta san cewa ƴan uwan Baban su Amra baza su yarda ba, ta san dole sai an yi rikici idan tace zata siyar da wannan gidan, Mama ta kasa runtsawa sai ma sallah da ta soma yi tana rage daren, bayan ta idar da sallan ta dinga rokon Allah ya kawo musu mafita, musamman ma a kan amra wacce take ganin tawayan ta zai sa da yawan mutane su cutar da ita, tana rokon Allah ya tsare mata ƴaƴanta har ta ga auren su ba tare da wani ya ci mutuncin su ba, Allah ya ba wa Amra Miji mai ƙaunarta wanda zai iya riƙe maraichin ta da kuma laluran da ke tattare da ita, Haka ta dinga kwararo addu'o'i kafin daga bisani ta kwanta a nan ƙasa Sabida a halin da Amra ta kwanta; zazzaɓi ne mai zafi ya rufe ta, ko ɗaga yatsa ba tayi, domin tsoratan da tayi da abun da Jabir yayi mata ya sanya ta a wani mawuyacin hali, abu kaɗan sai ta firgita, lokaci guda jikin ta ya rikice yayi zafi kamar garwashi Ba karamin tayar musu da hankali tayi ba sabida ganin yanda jikin nata ya rikice sai kuka take yi, Jiki na rawa Mama ta fita ta siyo mata magani ta bata ta sha bayan ta haɗa mata koko, Amma ko a haka jikin nata bai yi sauƙi ba, sai ma sake rikicewa da yayi, Ƙarshe kwanciya tayi a ɗaki ta ƙudundune jikinta, sai sannu suke mata gaba dayansu suna cikin damuwa sun kasa taɓuka komai, to dayake basu saba ganin ta a haka ba shi yasa hankalin su ya tashi ainun, Allah yasa ma yau asabar ne bata da aiki, ba ta zuwa ranan weekends Ƙarshe a haka ta wuni zugum a kwance jiki ya ƙi daɗi, duk maganin da ta sha daga ƙarshe sai dai ta amayo shi, Ga babu sauran kuɗi balle Mama ta kaita asibiti, shiyasa hankalin ta ya fi tashi sabida bata san ya zasu yi mata ba. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____ *AUSTARALIYA*        *SYDNEY* Wani irin yanayi SHAREEF ya shiga a wannan lokacin, sam ya kasa yarda da abun da ya gani bare ya gasgata a ƙwaƙwalwan sa, Cike da sanyin jiki ya zube a gefen Haseena yana sauke nimfarfashi kamar wanda aka koro yayi gudun ceton rai, Ya kasa kataɓus duk da yana jin yanda Haseena take kiran sunan sa, amma bai iya magana ba, kamar matacce haka ya koma, roƙon Allah yake yi a ransa Allah yasa abun da yake zargi ba gaskiya bane, to amma ga shi ya ji a zahiri, tabbas Haseena babu budurci a tare da ita, wurin a buɗe yake since bai sha wahalar shiga ba. He was confused and lost where to stop his thoughts in one place Haka itama Haseena, ta ɗauka cewa irin dad'i da gamsarwan da take samu wurin Nana babu kalansa a duniya, domin bata taɓa tunanin zata shiga wani yanayi irin hakan ba, wani irin mugun sha'awarsa ne yake taso mata, ko kaɗan bata gamsu ba ya sauka a jikinta, tana son ta jawo shi jikinta but ta gaza sabida rashin ƙwarin jiki, shiyasa tayi ƙoƙarin kiran sunan sa tana mai fashe wa da kuka sabida halin da take ciki Kukan nata ne ya soma dawowa da shi cikin hayyacinsa, har ya iya motsa jikinsa yana mai buɗe idanunsa lokacin da kukan nata ya dame shi, bazai iya jure jin sautin kukan ta ba, duk da yana a cikin wani hali, zuciyarsa zafi take mishi, ya rasa inda zai saka kansa sabida tunanukan da ke bijiro masa na zargin Haseena, tamkar ya haɗiye zuciya ya mutu tsaban kishi, Ɗakyar ya iya ɗago kansa yana sauke madaidaitan idanuwansa a kanta, wanda suke cike da zallan kishi gami da jin haushin ta a karon farko a rayuwarsa, ya so yayi mata magana sabida yanda ya ga tana kuka, sai kawai yayi ƙarfin halin tashi zaune yana sauke tagwayen ajiyar zuciya, tare da tariyo abun da ya wakana a yanzu, ransa na ƙara ɓaci kamar ya dunƙule hannu yakai mata duka haka yake ji, Bai yi aune ba ya ji hannayenta a jikinsa, har ta matso jikinsa tana kiran sunan sa; tare da furta "Please Dear help me, kar ka bar Ni don Allah, zan mutu." Hakan ne yasa ya sauke mata wani banzan kallo, murya a dishe ya kira sunan ta da ƙarfi yana furta, "Haseena, dama kin san wani ne kafin Ni?" Daram gabanta yayi mugun faɗi, take ta dawo cikin hayyacinta domin gaba ɗaya ta gama fita a hayyacinta; ita kanta bata san me take furta wa ba sabida tsananin sha'awar da ke damun ta, sai yanzu da ta ji saukar muryansa lokaci ɗaya ta wartsake tana buɗe idanunta A haukace yake furta maganar a yanzu, ga dukkan alamu zuciyarsa a wuya take, "I told you to wake up and explain to me how I will understand, kina ji na kin yi min shiru? Nace waye ya taɓa sanin ki bayan Ni Haseena? A yanda na same ki ba haka yakamata Virginia ta kasance ba, Who has seen before me?" Gaba daya ta rikice ta kiɗime ta rasa inda zata saka kanta tsaban tashin hankalin da ya bijiro mata, babu inda jikinta ba ya rawa, yawun bakin ta ma ya ƙafe ta kasa motsin kirki illa kallonsa da take yi a wani irin bahagon yanayi Yayinda shirun nata ya sake saka mishi shakku a cikin zuciyarsa, da wani irin yanayi yake kallonta kamar zai yi kuka a yanzu, nimfashin da yake shaƙa ma yana ƙoƙarin guje masa, idanunsa sun kaɗa sun yi jazur lokaci guda jijiyoyin wuyansa suka fito raɗo-raɗo, ɗakyar ya nuna ta da yatsa cikin ƙuncin da ya ziyarce shi, bakin sa na rawa yace, "Haseena, kenan maganata gaskiya ne? A buɗe fa na ji ki? It means wani ya taɓa shigan ki; ya shiga gonan da ba nashi ba? Tell me kar ki sa zuciyata ta buga yanzu in mutu a nan, ki furta min da bakin ki ya aka yi hakan ta kasance; ko amanata kike ci?" "Na shiga uku na lalace! Mai kake faɗa haka SHAREEF? Ban gane inda maganar ka ta dosa ba?" Tayi maganar a sa'ilin da ta miƙe zaune sabida tsananin tashin hankali da razanar da tayi, ƙarfin hali kawai tayi wajen ganin ta ɓoye damuwarta har ta iya furta masa wannan maganar cikin rawan murya Shi kuma jin tambayar rainin hankalin ta sai ya daka mata tsawa yana cewa, "You mean you don't know what I'm talking about? Na ce uban waye ya sanki kafin Ni? Wa kika bama kanki? Ai na san ba haka Budurwa take ba, cewa aka yi za a ji wurin a rufe sai an sha wahalar nemo wurin, kuma at the same time baza a iya shiga ba, but duk girma na lokaci guda na shige zuruf babu wani shamaki, to taya hakan ta faru? Za ki faɗa min ko sai na illata ki a nan wurin? Wlh idan kin ci amanata ne kin cuce Ni, kin cuci rayuwata, before ki kashe ni Ni zan kashe ki Haseena, da ke da ɗan iskan wanda ya shiga gonata duk sai na ci ubanku na kashe ku kowa ya huta." Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Tashin hankali kenan! Yanda SHAREEF ya rikice mata ya zare mata sabida tsaban kishi; ƙiris ya rage zuciyarta bata buga ba, kuka ta saka mishi jikinta na wani irin kerma tamkar an jona ta a shock, har haƙoranta haɗewa suke yi tsaban yanda take son magana amma ta gaza furta wa, Tuni ta sauko ƙasa ta duƙa a gabansa tare da ƙoƙarin riƙo masa ƙafa Amma sai ya janye ƙafafunsa yana miƙe wa tsaye a haukace, halin da ya shiga ma ya rasa mai zai yi ya huce, ko kayan jikinsa bai saka ba ya nufi hanyar fita tsaban ɓacin rai da kishin da ya haukata shi A guje ta tashi ta bi bayansa tana shan gabansa, cikin wani irin murya tana kuka take cewa, "wlh wlh SHAREEF ban san me kake zargi na a kai ba. Ban sani ba, Ni babu wanda na sani bayan kai a yanzu, babu wanda na taɓa bama kaina after you, ka yarda dani, ban san kowa ba, kai ne.. kai ne ka soma buɗe Ni, kai ne Allah..." Ta ma kasa maganar bare ta fahimtar dashi sabida kukan da take yi Shi kuma gani yake yi kamar ta gama raina mishi hankali, idan ya ci gaba da sauraron ta zai iya mata illa sabida yanda ya harzuƙa ransa yayi mugun ɓaci, Sai kawai ya juya ciki ya dauki kayansa ya soma ƙoƙarin saka wa Tana nan tsaye tana wani irin kuka mai tayar da hankalin mai sauraro, ta rasa ma me ke shirin faruwa da ita ne, tamkar a mafarki abun ke faruwa haka take gani, tabbas idan ta rasa SHAREEF mutuwa zata yi, zata iya jure komai amma ban da fushin sa, musamman a wannan gaɓar da in har tabar shi ya tafi, to; tabbas ta rasa shi na har abada, abun da yake zargin ta akai zai zama gaskiya, kuma ba zai taɓa waiwayo inda take bata Tana a wurin ya fito ya wuce ta a fusace kamar wani Zaki, haka ya nufi bakin ƙofa zai fice Amma sai ta bi bayan shi cikin sauri ta tare gabansa ta saka key a ƙofan, Juyowan da zata yi sai jin saukar marin sa tayi ya kakkaure ta da maruka har uku a lokaci guda, Take jin ta da ganin ta ya ɗauke ta tafi yuuu ta zube a ƙasa tana sakin wani uban ihu mai razanarwa. [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE2* _____Kafin ta dawo cikin hayyacinta; tuni ya koma ya ɗauki Jakar kayansa da yake yashe a cikin Falon, ya buɗe ƙofan ya fice a mugun fusace; ko damuwa da duhun da ke gari bai yi ba, haka ya fice a gidan ya bar ƙofofin a buɗe Inda Haseena na yashe a ƙasa babu kaya a jikinta, sautin marukan da yayi mata sai amsa kuwa suke mata a cikin kunne, tunda uwarta ta haife ta bata taɓa jin azaba makamanciyar irin wannan ba, sosai marukan da yayi mata suka ɗimauta ta suka fitar da ita gaba ɗaya a cikin hayyacinta, wani irin kuka ta saka har yanzu tana kwance ta gaza buɗe idanunta sabida azaban da ke ratsa ta, Kukan kawai take yi kamar zata shiɗe don azaba, tana jin tamkar yanzu ne ake marin ta domin yanda wurin yake mata zafi ko hannayenta ta kasa cire wa a wurin, Tsawon lokaci tana a haka before ta buɗe jajayen idanuwanta cikin kuka ta soma yunƙurin tashi zaune, babu inda jikinta ba ya rawa, take ta sake mayar da hannayenta a wurin domin ji take yi kamar an sauya mata halittar kumatun ta, wurin ne ya kumbura suntum har da shatin yatsunsa, domin ba ƙaramin mari ta sha ba a wurin SHAREEF, abun da bata taɓa tunani ba, wai yau ita SHAREEF ya mara, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Ba marin ya fi ɗaga mata hankali ba illa tafiyar da yayi ya barta, Daƙyar ta iya mike wa ta isa cikin bedroom tana neman kayan da zata saka, kuka sosai take yi ko saurara wa kanta ba ta yi, domin hankalin ta idan yayi dubu to ya tashi, ba ta jin zata iya rayuwa babu SHAREEF a tare da ita, ƙaunar da take masa hakan bazai taɓa sa ta rabu da shi ba, Tabbas a yau tana tsananin cikin dana-sanin aikata zunubin da tayi, bata taɓa tunanin kasancewar ta da Nana zai sa har SHAREEF ya gane ba, kenan ta rasa budurcin ta batare da ta mu'amalanci namiji ba? Dama hakan tana iya kasancewa ne? Wani sabon kuka ta fashe dashi tana ɗaura kanta a saman gadon, while jikinta na a ƙasa tana ta sharɓan kuka, ta rasa ma me ke mata dad'i babu inda jikinta ba ya rawa, cikin kukan take cewa, "don Allah SHAREEF ka dawo gare Ni, bazan iya rayuwa babu kai ba, kai kaɗai nake so, kayi min alƙawari ko mene ne baza ka taɓa iya rabuwa dani ba, ba laifi na bane, Ni kaina ba a san raina na aikata wannan zunubin a gare ka ba, babu yanda zan yi ne, wlh bazan taɓa iya rabuwa da kai ba." Sambatu ta dinga yi kamar wata mahaukaciya, gaba ɗaya ta kasa sararawa kanta jin ta take yi tamkar ta kashe kanta don baƙin ciki, "Ka yi hakuri don Allah SHAREEF, ban taɓa aikata zina ba, ban san hakan zai kawar min da budurcina ba, Nana ce ta cuce Ni, Ni ban san meyasa na biye mata ba." Idanunta jazur sun gama kumbura sun yi suntum, ta gaza yin shiru haka take ta sambatu kamar akwai SHAREEF ɗin a gabanta, miƙe wa tayi ta nufi ƙofa zata fice, sai dai yanda ta ga gari yayi duhu alamun dare ya tsala, baza ta iya fita a haka ba, tsoro bazai bar ta ba, don haka ta rufe ƙofan tana koma wa daki ta ɗauki wayanta, kiran layin SHAREEF ta soma yi, tun farko da ya shiga yayi rejected tare da kashe wayan gaba ɗaya, koda ta sake kira sai ta ji a kashe, kuka ta dinga yi ta kasa runtsa wa a daren nan, wayanta na a hannunta lokaci kaɗan ta dauka ta kira sa, but abu ɗaya ake faɗa mata wayan a kashe; amma ta kasa hakura, babu irin text na bada haƙurin da bata tura masa ba, amma babu reply, ƙarshe a haka ta kwana a ƙasa batare da ta san lokacin da barci ɓarawo ya sure ta ba. *** _____Kai tsaye SHAREEF hotel ya wuce ya kama ɗaki, tunda ya shiga ya rufe kansa ya kwanta bai sake motsa wa ba, kamar matacce haka ya koma, hawayen da ke fita a kwarmin idanunsa su kaɗai zasu tabbatar da cewan yana raye, abun yayi masa ciwon da har ya kasa bama kansa damar yin wani tunani, tamkar ya haɗiya zuciya ya mutu haka yake ji, musamman in wasu tunanuka suka bijiro masa a kan Haseena ta ci amanar sa, kuma bai san tun tsawon lokacin da ta ɗauka tana mu'amala da Maza ba bayan shi, duk irin son da yake mata da tattalin zuwan wannan ranan, ashe wani ya riga sa? Maiyasa Haseena zata ci amanarsa irin haka? a karon farko; a karon farko ya soma jin nadamar sanin ta a rayuwa, Shi mutum ne mai tsananin zafin kishi, zai iya yin komai a kan abun da yake so, idan yace komai; to yana nufin komai, shiyasa dole ya hassala ransa yayi mugun ɓaci, wani irin kishi mai zafi ya turniƙe shi wanda yasa ya kasa control kansa, Da zafin zuciyar ya kwana a wannan halin tamkar matacce har garin Allah ya waye, kuma bai runtsa ba ko kaɗan, bare shi ba mai ibada bane balle ya nemi sassauci wurin Allah; yanda ka san kamar zai cire zuciyar ya yasar tsaban tafarfasan da take mishi, Har safe yayi ya kasa tashi sabida yanda ya ji jikinsa ya saki ga wani irin ciwon kai da ya kawo mishi mamaya, zazzaɓi ne mai zafi ya soma kama shi sabida yanda abun ya tsaya mishi a rai zuciyarsa ta jagule tamkar zata fito ƙirjinsa don zafi da raɗaɗi, Ko sallah ya kasa yi a haka ya zauna har rana, Daƙyar ya iya samu ya tashi jiri na son kayar dashi, a haka ya shiga toilet ya daura alwala idanunsa sun canza kala face ɗin nan ta ƙara jazur da ita duk ta kumbura, sallan asuba ya gabatar ya haɗa dana azahar sannan ya koma ya sake rafke wa zuciyarsa na tafarfasa; a duk second ɗaya idan ya tuna abun da Haseena tayi masa ji yake yi tamkar ya mutu, Dole ya koma ya tuhume ta a kan wanda ta ba shi kanta, domin bazai taɓa samun sukuni ba muddin bai aikata abun da ke zuciyarsa ba. *** _____Haseena tana kwance itama har garin Allah ya waye ba tare da ta farka ba, wani wahalallen barci take yi mai cike da mafarkai kala-kala a kan SHAREEF; tunda shi ne ya tsaya mata a rai, Wayanta ne ta soma Ring; wadda ta sa lokaci guda ta farka a gigice, A tunanin ta ko SHAREEF ne shiyasa nan da nan ta wawura wayan tana duba screen ɗin, sunan Nana da ta gani shiyasa ta ajiye wayan jiki a sanyaye, Ƙin ɗaukar wayan tayi duk da tana jin kiran da take mata, almost three missed calls before ta dakata Sabon kuka ta saka a lokacin tuna abun da ya faru jiya, wi-wi haka take kukan domin tana jin baza ta iya yafe wa kanta ba in har SHAREEF bai yafe mata ba, taya ya zata iya rayuwa mai daɗi babu shi a kusa da ita? Fushi fa yake yi da ita; wanda hakan bai taɓa faruwa ba, A nan ta wuni tana kuka ta kasa yin komai sai duba wayanta da take yi tana sake neman layin sa, but har yanzu switch off ake ce mata, Tabbas in har bai yafe mata ba baza ta taɓa iya zama a ƙasar nan ba, dole ne ta koma gida, ta je ta ba shi haƙuri ta faɗa masa gaskiyar abin da ke faruwa, ita bata taɓa sanin wani namiji ba, wlh bata taɓa sanin son da take mishi ya zarce haka ba sai a yanzu da ta san cewa ta rasa shi, ji take yi kamar tayi hauka, tabbas baza ta iya rayuwa babu SHAREEF ba, soyayyarsa ya bi jinin jikinta ya zama tsoka a jikinta, fushin sa babban illa ne a gare ta, Tashi tayi ta shiga toilet tayi wanka shaf-shaf ta fito, ko tsaya shafa komai bata yi ba ta soma haɗa kayanta a trolly; after ta zura doguwar riga mai sulɓi da mayafinta. dama rabon da tayi sallah ta manta, sai idan ta ga dama ne zata haɗa su dukka a lokaci guda ta rama, yanzu kuwa hankalin ta a tashe yake bata da time, Tana jin wayanta tana ƙara but ta ƙi ɗauka tunda ta tabbatar da Nana ce, ga yunwa da ke addabar ta amma bata bi ta kai ba; ta ja trolley ɗin ta zuwa Falo, komai na na'ura ta kashe sannan ta fice zuwa waje, Wurin Motanta ta nufa, but bata kai ga shiga ba sai ga Nana ta shigo gidan, Hango ta da tayi shiyasa tayi saurin ƙarisa wa wurin motan tana buɗe wa da sauri ta jefa Jakar ciki, sannan ta zagaya zata shige motan Sai dai tuni Nana ta iso wurin ta tana kiran sunan ta cikin mamaki, "Haseena, where are you going now?" Daurewa Haseena tayi ta juya tana kallon ta fuskarta babu walwala Sosai Nana ta tsorata da ganin yanda fuskar Haseena ta koma, ta kumbura suntum ga shatin yatsu alamun an mare ta, idanuwanta sun canza kala sun yi jazur, That's why one time Nana got confused and asked what was bothering her? Tuni ta kamo hannunta a rikice cikin tashin hankali Amma sai Haseena ta kaɓe hannunta, lokaci guda hawayen da take riƙewa suka soma zuba a kan face ɗin ta, cikin rawan murya take cewa, "Leave me for God's sake, I will go, daga yau babu Ni babu ke, from today I am gone, don't come to my place again, domin tarayyana da ke babu alkhairi, a kanki zan rasa wanda na fi so da ƙauna, sake Ni." Ta sake janye hannun tana share hawayenta tare da ƙoƙarin juyawa ta shiga Motan Amma sai Nana ta sake riƙo ta da ƙarfi sabida ranta ya ɓaci da jin kalmomin Haseenan, take tayi amfani da tsafin ta wurin control ɗin ta, suna haɗa ido lokaci guda idanun Nana suka juye zuwa ja wani walƙiya suka soma fitowa suna shiga idanunta Take a nan jikin Haseena ya saki, nan da nan ta kama kanta sabida wani irin jiri da yake ƙoƙarin ka da ita, sai kawai ta zube a jikin Nanan a sume babu numfashi a tare da ita Ita kuma sai ta ɗauke ta zuwa cikin gidan ta shige da ita tana rufe ƙofan. ***            _____Sai bayan la'asar sannan SHAREEF ya iya tashi; sabida ganin zai iya mutuwa idan har bai nemi abu ya saka a cikin sa ba, jikinsa har rawa yake yi saboda rashin karfin jiki ga tsananin zazzaɓi da ke jikinsa, to ya ɗaura wa kansa jarabar tunani da damuwa zuciyarsa kamar zata fashe don bala'i da ƙunci, Abinci yayi oda ya zauna ya ci duk da daƙyar yake iya tusa wa a cikin sa, ko rabi bai yi ba haka ya miƙe ya shiga yayi wanka ya canza kayansa; sannan ya ɗauki Jakarsa ya nufi airport, Koda ya je babu jirgin Nigeria a lokacin, sai ƙarfe goma na dare sannan za a samu, Dalilin da yasa ya dawo hotel ɗin kenan, ya ci gaba da kwanciya har time yayi, sallah kaɗai ke ɗaga sa, ya so ya koma wurin Haseena ya tuhume ta don zuciyarsa ta kasa natsuwa, amma kuma ya fasa sabida a lokacin wani irin haushin ta yake ji, sam ba ya son sake tozali da ita, a rayuwa shi mutum ne wanda ba ya son a ci amanarsa, musamman a kan abun da yake so, kishin da yake dashi zai iya aikata komai a kanta, yana tsananin ƙaunar Haseena wanda baki ma bazai iya misalta wa ba, shine dalilin da yasa yake tsananin kishin ta kuma zai iya yin komai ko mene ne kuwa, Amma sai ga shi yau ita ya kama da cin amanarsa, already ta fifita wani a kansa, idan har ta san haka ne meyasa tun farko ta aure shi? Dama ta san ba shi kaɗai zata iya zama dashi ba amma ta ɓata mishi lokaci har haka? Fushin da yayi da ita ba na wasa bane, duk da ba ya jin zai iya rabuwa da ita amma dole ya ɗanɗana mata kuskuren ta, idan ya je ya huce da ƙafafunta sai ta zo ta ba shi hakuri sannan zai ɗauki mataki a kanta Yana ganin ƙarfe tara tayi ya nufi airport ya zauna a can, har sai da aka kira su sannan ya shige jirgin Basu isa Nigeria ba sai a washe gari da tsakar rana, Keke napep ya hau ya isa dashi gida, Time ɗin da ya shiga Falo Momy ne kaɗai zaune Tayi mamakin ganin sa a haka duk da yau Lahadi zai dawo, amma a yanda ta ganshi tamkar an jeho shi babu natsuwa a tare da shi, abun ya ɗaure mata kai, shiyasa bayan ta amsa gaisuwar sa take cewa, "lafiyar ka dai SHAREEF? Wani abin ya faru ne?" Girgiza mata kai yayi yana ƙoƙarin ɓoye halin da yake ciki, sai yace, "No Momy babu komai." Shiru ta ɗan yi, duk da bata yarda ba kasancewar ta san waye SHAREEF, kamar ta tambaye shi Haseenan; sai kuma ta fasa tana taɓe baki tare da cewa, "ok, ka shiga in ka kimtsa ga fruit salad nan sai ka sha; before in gama abinci." Bai ce komai ba ya juya ya wuce steps zuwa dakin su, yana shiga bedroom ya tarar da Hanif yana shirga barci, yayi ɗai-ɗai abun sa daga shi sai gajeren wando a jikinsa, babu riga ya ƙure AC yana shan iska, Jakarsa ya ajiye yana zama a gefen gadon, tare da tallabo kansa da ke barazanar tarwatse wa sabida mugun tunanin da ya addabe sa, har wani biji-biji yake gani a idanunsa, kasa jurewa yayi shiyasa ya kwanta a saman gadon yana sauke numfashi mai ƙarfin gaske Sama-sama Hanif yake jin motsi a kusa dashi, har hucin numfashi yake ji shiyasa ya farka a nan take. Mamakin ganin SHAREEF yayi kwance yana sauke numfarfashi kamar wanda bai da lafiya, hakan ya tsorata shi shiyasa yayi saurin tashi yana kai hannunsa jikinsa tare da cewa, "Bro lafiya dai? Yaushe ka dawo?" Buɗe idanu yayi ya sauke masa su a cikin nasa, sun yi ja idanun ko da gani ka san yana cikin tsananin damuwa Shi kansa Hanif ya san ba lafiya ba a yanda ya gansa a hargitsen nan, ga jikinsa da zafi da ya taɓa har kerma ya ga yana yi, that's why ya ɗan ruɗe da tambayarsa cikin damuwa da son sanin me ke faruwa dashi But SHAREEF ya kasa magana illa miƙe wa zaune da yayi yana ci gaba da sauke numfashi, tare da ƙoƙarin daure wa ciwon da ke sukan shi "Please Bro ka sanar min me ke damunka? Ka ɗaga min hankali; tell me what's wrong with you?" "Nothing, kawai kaina ke min ciwo." Yayi maganar a hankali cikin sanyin muryansa, yayinda ya kama kan ya kasa saki Shi kuma Hanif cike da damuwa yace, "I'm sorry, ina zuwa bari in dauko maka magani ka sha." Ya sauka a kan gadon yana koma wa wurin dressing mirror, since a nan suka fi yawan ajiye magani, ɗauko masa na ciwon kan yayi tare da fita zuwa Falo ya buɗe fridge ɗin, roban ruwa guda ɗaya ya gani a ciki, shi ya ajiye ma ɗazu, shiyasa ya dauka ya kawo masa yana miƙa masa yace, "ya sha." Babu musu SHAREEF ya amsa ya shanye since yana jin jiki sosai, buƙatar sa kawai ya samu relief Zama Hanif yayi a gefen sa yana kallonsa, sai ya ɗan ja numfashi cike da tausayin sa yace, "tell me what's wrong with you? I know akwai abun da ke damunka ba ciwo kaɗai bane, kana cikin damuwa Bro alamun ka ya nuna min." Shiru SHAREEF yayi ya kasa yin magana, duk da ya san cewa ba ya iya ɓoyewa Hanif komai, amma yau yana jin kamar bazai iya sanar mishi wannan sirrin ba, tabbas babban sirrin sa ne; taya ya zai iya sanar mishi? Tunanin da ke ransa kenan Amma sai Hanif ya dage yana lallaɓa shi domin ya damu da son sanin abun da ke damun ɗan uwan nasa, hankalinsa ya soma tashi a kansa Hakan ne yasa daƙyar ya iya buɗe baki ya sanar mishi da komai, idanun nan sun sake kaɗa wa sun yi jazur, sai ga ruwan hawaye suna fita, yana kallon Hanif ɗin yake cewa, "ban taɓa tunanin wannan abun zai kasance ba, Haseena fa, wacce nake ƙauna na bata yarda ta gaba ɗaya, amma yau ita ce ta ci amanata, ta wulaƙanta Ni, na kusance ta amma na ji ta a buɗe ba a yanda Mace zata kasance ba, wani ta bama kanta yayi amfani da ita bayan gani tsawon lokaci abun da nake jira ban samu ba." Sai ya ja numfashi yana kai hannunsa tare da share hawayen da ke gudun tsere a kan face ɗin sa Tausayi da tsananin mamaki gami da tunanin girman son da ɗan uwansa yake yi wa Haseena; shine a zuciyar Hanif, tabbas yana jinjina wanne irin soyayya ne SHAREEF yake yi wa yarinyar nan da har yau yake zubar da hawaye a kanta? Shi kansa ya ɗan rikice da jin zancen; amma kuma sai ya dafa SHAREEF ɗin cike da sanyin murya yace, "Bro, Ni ban gane wanne irin buɗe wa kake magana ba? A yanda na san Haseena tana kaunarka, in har bata baka kanta ba bana tunanin zata iya bama wani kanta, a tunanina kun daɗe da sanin juna ba wannan karon bane, ashe kallon da nake muku ba haka bane?" Wani kallo SHAREEF ya watsa mishi, sai dai bai ce komai ba ya ɗauke idanunsa tare da sanya hannu ya buga tagumi "To amma kai taya ya ka san cewa a buɗe take bayan baka san wata Mace ba? Ka san buɗe wa kuwa?" "Kana son ka raina min hankali ne? Ina maganar serious issues but kana son ka mayar dani tamkar ban san me nake yi ba? Zuruf abuna ya shige duk girmana, taya ya kake tunanin bazan yi wannan zargin ba?" Wani irin dariya ne ya so kufce wa Hanif sabida abun da yace; amma kuma tuni ya riƙe dariyan a cikin sa gudun samun matsala; sabida yanda SHAREEF ɗin yake a fusace ya san tsab zai iya ƙara harzuƙa shi yakai mishi bugu, duk da haka sai da ya murmusa yana kawar da kansa gudun ya gansa But bai san SHAREEF tuni ya gane sa ba, shiyasa ya buge hannunsa da ya ɗaura masa a kafaɗa yana cewa, "kana min dariya since ka mayar da Ni mahaukaci?" "No ba haka bane Bro, abu ne dai da ayar tambaya a ciki..." Kasa ƙarisa maganar yayi ganin kallon da SHAREEF yake masa a yanzu Dogon tsaki ya ja yana mike wa tare da faɗin, "ba na son ma maganar a barta, ka ci gaba da dariyan kai kaɗai tunda ka mayar da Ni sakarai." Toilet ya nufa ya shige yana bugo ƙofan Yayinda Hanif ya fashe da dariya yana toshe bakin sa, "Oh! Bro matsala, yau dai abun bai yi dadi ba, yarinyar da ka ƙwallafa rai a kanta an samu akasi ta ci amanarka, dama koda ganin wannan yarinyar tana fiƙi-fiƙi da ido za a rina ai". _Fan's fatan an yi zaɓe lafiya? Allah ya zaɓa mana shuwagabanni na alkhairi waɗanda zasu sadaukar da lokacin su domin kawo ci gabanmu Amin._ 19 March 2023. [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE3* _____Biji-biji ta soma gani har sanda ta wartsake ta soma ganin ɗakin, a hankali ta mayar da idanun nata tana lumshe su tare da sake buɗe su, nan take ta sauke su a kan face ɗin Nana da ke zaune saman sofa ta harɗe ƙafafu tana kallonta Murmushi tayi mata tana tasowa ta zo inda take, tare da kai hannu tana shafa mata face da faɗin, "babe, kin tashi?" Haseena ta kasa yin magana saboda yanda take jin jikinta tamkar ba nata ba, kanta juya mata yake yi in ta rufe idanu sai ta soma ganin ja kamar da halittun mutane sun yi dandazo harshen su na zubar da jini, take wani tsoro ya soma kama ta sabida ji take yi kamar suna mata dariya, ta kasa yarda cewan mutane take gani idan ta rufe idanun, shiyasa ta sake rufe wa don ta gasgata, tabbas ta tabbatar da cewa mutane ne take gani suna zaro harshe suna mata dariya a ƙwayar idanunta, exactly waɗanda ta gani a mafarki before ta farka, amma abun da ke bata mamaki yadda ta ga har da Nana a cikin mafarkin, ita ta janyo hannunta zuwa wurin mutanen da ta kasa bambance fuskokin su sabida tsaban mugun ɓaci da suka yi da jini, harshe a waje suna dalalar da jini, Gani tayi sun yi mata ƙawa sun ɗaura ta a kan dogon kujera, Nana ta amso kwarya mai faɗi a hannun wani ƙaton mutum mai dogon gashin kai, sai ta taho wurin ta ta soma bata a baki ba tare da tayi mata magana ba, Kamar sokuwa haka take shan abun ciki tana kallon Nanan har sanda ta shanye, While ita kuma Nanan tana mata murmushi har sai da ta gama bata ta janye ƙwaryan, sai ta bushe da wani uban dariya tana jefar da ƙwaryan cikin tsananin farin ciki tana furta, "Barka da zuwa ƙungiyarmu Haseenaaaa." Daga nan ne ta ji idanuwanta sun soma buɗewa har ta wartsake, a tunaninta mafarki ne amma kuma idan ta rufe ido a yanzu tana hangen mutanen, hakan ne yasa firgici ya shige ta ko iya amsa maganar da Nana tayi mata bata yi ba, wai ta sake rufe idanun don ta gasgata abun da take gani, zahiri halittun take gani da zaran ta rufe idon, shiyasa ta miƙe zaune da sauri tana zare ido cike da tsananin tsoro tana kallon Nanan; da ke gabanta har yanzu tana zuba mata murmushi, sai dai kuma yanda ta ga idanuwanta suna ƙyallin wuta; hakan ne yasa ta soma shiga tashin hankali da tunanin abun da ke shirin faruwa Hannu Nanan ta sanya tana kamo nata tare da riƙe mata su gam, wani irin murmushi take zuba wa tana kallon cikin ƙwayar idanunta, tare da kiran sunanta da cewa, "Haseena, ina miki maraba da shiga cikin mu, a yau ina cikin farin ciki matuƙa, Of course I love you very much in my heart, I can't be separated from you, na san kema baza ki taɓa watsa min ƙasa a ido ba, kar ki damu kowancce irin damuwa naki ta ƙare daga yau." Shiru Haseena tayi tana kallonta kamar sokuwa, a hankali tsoron da ke tattare da ita ya soma fita a jikinta, tana jin wani irin baƙon yanayi a tare da ita, sai dai ta kasa gane inda maganar Nana ta dosa, tana kallonta ta saki hannunta tare da dunƙule hannunta sai ga shi ta miƙo mata sweet "Take it." Kamar kar ta amsa, sai kuma ta kasa mata musu, ta amsa tana buɗe wa a hankali ta saka a baki Smile tayi tana shafa mata cinya a hankali, Zara-zaran yatsunta ta kafa mata tana zagaye mata cinyoyi cikin wani irin salo na jan hankali Lumshe idanu Haseena ta soma yi tana jin yanda salon ke tafiya da ita, tana jin wani irin daɗi na shiganta, ta kasa buɗe idanu bare ta hana Nana abun da take mata, Sai dai kuma tunanin SHAREEF da ya bijiro mata; nan take ta tuna abun da ya faru before yabar gidan, saurin ture Nanan tayi a jikinta, wadda ta maƙale mata kamar wata Mage tana lashe ta, cikin tashin hankali take kallonta da faɗin, "na shiga uku! SHAREEF ya tafi ya bar Ni. He left Me forever." She ended the conversation crying a lot Tallabo ta Nana tayi tana cewa, "Please stop crying, let me know what happened, why did I see you go and get your trolley?" Cikin hawaye take bata labarin abun da ya faru, and take ƙare maganar da furta, "ke kaɗai na sani ban san wani namiji ba, amma sanadin haka zan rasa shi, bazan iya jure rabuwa dashi ba, shi ne rayuwata, Please help me ban san yanda zan yi in dawo dashi cikin rayuwata ba." Ɗaure fuska Nana tayi tana kallonta, sai tace, "meyasa kika kasa fahimta na ne har yanzu Haseena? Na sanar miki cewa babu irin wannan alaƙar tsakanin ki da shi, duk abun da kike so ina miki and I told you. The life of a woman and a woman is more pleasant, the case of lesbianism is more pleasant than anything else now, you will be happy without any worries, ina kishin ki bazan iya bari ki ci gaba da alaƙa dashi ba, ki bar shi za ki ji daɗi a rayuwa in kina tare da Ni, zan wadata ki da farin ciki, you will get a lot of money and happiness, remove love from your heart and live our life together." Girgiza kanta Haseena tayi tace, "No, I told you it is my life now, bazan iya rabuwa dashi ba. I can lose all my happiness, I love him and I love him to the heart, SHAREEF ya zama Ni gaba ɗaya, bazan taɓa iya barin ma wata Mace shi ba, help me find him please, yayi fushi dani ya tafi bazan yi farin ciki ba in har babu shi tare da Ni." "Ok, ok, don't worry. I want everything you want, in har SHAREEF ne za ki same shi, zan taya ki yaƙin samun shi na har abada, sai dai da sharaɗi, and you know I love you so much, I will do anything for you." Ta ƙare maganar tana kashe mata ido daya Murmushi Haseena tayi tace, "what should I do if you help me, ina son na samu SHAREEF ya zama nawa na har abada, shine duniyata yanzu, shi kaɗai nake so a raina." Nana tace, "And what position did you put me in? Don't you love me?" "I love You so much, ban san yanda zan nuna miki yanda nake jinki a raina ba a yanzu, but ina jin tamkar mun jima tare da juna, I don't know why I need you more than anyone else with me, I really need you." Tayi maganar tana mai ɗaura kanta a jikin Nanan, tare da lumshe idanuwanta sabida jin tsananin sha'awarta da ke ƙoƙarin taso mata Hannu Nanan ta sanya tana shafo ta cikin yanayin duniyanci, while takai bakinta zuwa kunnenta tana raɗa mata maganganu masu tayar da hankali cikin ƙwarewa da son burkita mata lissafi A hankali kuwa Haseena ta soma biye mata suka soma aikata abun da suka saba; cike da ƙaunar juna da wani irin shauƙi mai fizgar hankali, Lokaci guda Haseena ta soma manta damuwar da ke tattare da ita suka tsulma gogin aikata masha'a cike da son zuciya da kuma *RUƊIN DUNIYA* (My Book). 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____Wasa-wasa ciwo ne ya rafkar da Amra a cikin wadannan kwanakin da suka shuɗe, zazzaɓi mai zafi tayi fama dashi duk don a kan abun da Jabir yayi mata, ta tsorata dashi ba kaɗan ba Duk yanda Mama take kwantar mata da hankali tare da mata nasiha mai ratsa zuciya, amma abun ya faskara jikin nata ya ƙi daɗi ta kasa cire abun a ranta, Ita kanta Maman ta fita shiga damuwa, tunda ta san cewa abun ya taɓa Amran ne, tana tausaya mata kasancewar halin da take ciki na lalura, su kansu su Afra walwalan su ta ragu tunda suka ga yadda Yayarsu take fama da jiki Ranan Monday ma Mama tace, "ta haƙura kawai da aikin tunda jikinta babu daɗi har yanzu, bazai yiwu a ce ta fita a haka ba gwara ta hakura ko zuwa gobe ne sai ta je." Amma Amra sai tayi mata bayani cikin kurmancin ta tace, "zata iya zuwa kar ta rasa aikin ta, ba ta son a kore ta su rasa damar su." Sai ta yi wa Maman murmushi cikin ƙarfin hali da nuna jarumtar ta take sake mata bayanin, "ta ji sauƙi ma zata iya zuwa, kawai rashin ƙarfin jiki ne." Duk da Mama bata yarda ba but bata da yadda zata yi, don itama tana gudun su rasa wannan aikin wanda dashi suka dogara a yanzu, shiyasa ta saka ta a gaba sai da ta cinye tuwon da ta sawo mata, sannan ta bata magani ta shanye, ta zuba mata sauran a Jaka tayi mata bayanin, "idan ta je can, zuwa anjima sai ta sake sha." Dubu ɗaya ta bata ta gargaɗe ta, "ta siya wani abu ta ci kar ta zauna da yunwa." Murmushi Amra tayi tana gyaɗa mata kai alamun ta ji, sannan ta miƙe ta karisa shirya wa suka fita da su Afra tunda suma sun gama shirin Makaranta, Suka fita tare suka hau keke napep ɗaya kasancewar hanya daya suke bi, but su Afra za a fara sauke wa kafin ita, Shi yasa Afra ta yiwa Mai napep ɗin bayani sannan suka shiga ya ja su Har bakin makarantar su Afra ya sauke su, Suka fita suka yi wa Amra sallama suna ɗaga mata hannu, itama tana ɗaga musu tana ta washe musu baki har suka tafi Bakin Companin ya ajiye ta sannan ta sauka ta shige cikin Companin da ɗan saurin ta; kasancewar tayi late ma, A lokacin da ta shiga office din su, secretary shima bai zo ba alamun yayi late ne, amma office din Hanif a buɗe yake, hakan ne ya bata tabbacin yana ciki, shiyasa ta nufi wurin tana sake maƙale Jakarta da ke hammata, hannu tasa tayi nocking, sai da ta ji ya bata iznin shiga sannan ta tura ƙofan ta shige ciki he is sitting on his chair facing her, idanu ya zuba mata yana kallonta har ta zo ciki ta zauna a kan kujera; bai ɗauke ido a kanta ba sabida ganin yanda ta sauya masa a ɗan kwanaki biyun nan, idan idanuwansa ba ƙarya suka yi masa ba ya ga ta rame sosai kamar tayi ciwo, har siraran laɓɓanta sun bushe gefen bakin da hucewar mura, Wani iri ya ji a ransa duk da bai tabbatar da cewan ga abun da ke faruwa da ita ba, amma har ransa ya ji damuwa da tausayinta Ita kanta yanda yake mata wannan kallon; yasa ta kasa cewa komai, illa sauke kai ƙasa da tayi tana mamakin irin kallon ƙurillan da yake mata, hakan ne yasa har gabanta faɗuwa yake yi haka kawai ta ji wani irin yanayi a tattare da ita, wanda yasa ta kasa motsi tunda ta duƙar da kanta "Amrah." Ya kira sunanta cikin wani yanayi ba tare da ya dena kallonta ba A hankali ta ɗago kanta ta zuba ƙwayar idanunta cikin nasa, sai dai tuni tayi saurin ɗauke su sabida yanda ta kasa jure irin kallon da yake mata, ta rasa wanne irin yanayi ne ke baƙuntan ta a wannan lokacin Sake magana yayi a hankali kamar yana tsoron wani ya ji, inda ya taso da jikinsa daga jikin kujeran yana ɗaura hannayensa biyu a saman teburin tare da furta, "ciwo kika yi ne haka; na ga kin rame ne kamar kin yi ciwo? What's wrong with you?" Sai ya janyo Memo da ke gabansa ya haɗa da bairo ya miƙa mata tare da furta, "oya tell me, me ke faruwa ne?" Hannu tasa ta ɗauki Memon batare da ta ɗago ta kalle sa ba, kamar baza tayi rubutun ba kuma sai ta soma rubuta mishi, "bani da lafiya ne, amma na ji sauƙi." Bayan ta gama sai ta tura masa gabansa tana kallonsa Karanta wa yayi yana duban ta, tuni face ɗin sa ta sauya cikin ƙanƙanin lokaci, cike da tausayin ta yake faɗin, "eyya sorry, I didn't know you were sick, da nazo har gida na duba ki, kuma na san kina da numbana meyasa ba ki kira Ni ba?" Shiru tayi tana duƙar da kanta da barin kallonsa "Kin yi shiru tell me? Ko dai ma bani da matsayin da za a iya ajiye numbana ne?" Ya ƙare da ƴar barkwancin sa yana son jin mai zata ce, yayinda ya sanya hannu a aljihu yana ɗauko wayansa ya sake duban ta da faɗin, "kin yi shiru; maganata ta zama gaskiya kenan?" Murmushi tayi tana girgiza masa kanta alamun a'a Numban ta ya nemo a wayansa yana miƙa mata tare da cewa, "Ni kinga me nasa a numban ki, sabida matsayin da na ba ki My sister na rubuta." Kallon wayan tayi tana murmusawa, har zuciyarta ta ji daɗin sunan bata san meyasa ba "Amma ke na san maybe ma ban samu matsayin suna ba, cuz na san haka Mata kuke yi, don haka ina son sanin me aka sa min a sunana?" Ɗan waro ido tayi tana dariya wadda ya bayyana jerin haƙoranta, sai kuma ta duƙar da kai sabida kallon da yake mata cike da kunya Shima murmushin yayi har ransa ya ji dadin yanda ta saki jikinta, hakan ne yasa ya ƙara cewa, "ki bani in gani mana, sai kin nuna min fa." Maƙe kafaɗa tayi da sauri Shiyasa ya bushe da dariya yana cewa, "ba ki da gaskiya ko?" Rufe idanunta tayi da hannayenta sabida kunya Shi kuma sai yayi shiru bai sake cewa komai ba, amma ya kafa mata idanu yana jin wani irin farin ciki a ransa, bai san meyasa yarinyar ta tsaya mishi a rai ba a yanzu yake fama da tunanin ta, ji yake yi kamar su dauwama a haka sabida yanda yake jin nishaɗi, Ɗago kan da tayi suka haɗa ido, sai tayi saurin mayar da kanta, murmushi shi kuma yayi yana cewa, "please don Allah ki bani matsayin ko Yaya ne a zuciyarki, ina son ki taimaka ki bani wannan matsayin, duk sanda ba ki da lafiya irin haka ki yi ƙoƙarin kirana; ko ba komai na san zan iya taimaka miki, ba sai kin zo office ba, i know daga ganin ki ba ki samu sauƙi sosai ba amma kin zo, kar ki sake irin haka kinji?" Ɗago kai tayi tana duban sa tare da gyaɗa masa kanta cike da girmamawa, ba ƙaramin daɗi ta ji ba da furucin sa Murmushi yayi mata yana duban agogon hannunsa, sai ya sake kallonta yace, "secretary he not come today, and we have a meeting now, zamu iya tafiya yanzu." Miƙe wa suka yi a tare, ya soma yin gaba sannan ta bi bayanshi har zuwa hole ɗin da suke taro, Sai dai a tunanin Hanif zai ga SHAREEF ya zo since ya bar sa a gida ya ƙi biyo sa, amma ga shi bai zo ba, yana can gida ya ɗaura wa kansa damuwar Haseena, shiyasa da ya gaji da lallaɓa sa ya taho abun sa, Yanzu kuma ga shi zasu yi meeting na amsar wasu sabbin gwangila but bai zo ba, Ba yanda Hanif ya iya dole suka yi taron, Sun ɗauki kusan awa ɗaya before su kammala kowa ya watse suka koma bakin aiki. [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱          *SHAREEF*              _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE4* _____After Hanif ya tashi, bai bari Amra ta tafi ba yau da kansa yace, "zai kaita domin ya ga gidan su, ko don idan wani abu ya taso." Da farko ta ƙi amincewa since bata so hakan ba, Amma da ya matsa mata dole ta yarda ta kasa ci gaba da masa musu, haka ta haɗa komai sannan ta ɗauki Jakarta ta saka shi a hammata ta bi bayansa zuwa bakin motansa, Gaba ya bata umarnin ta shiga after ya buɗe mata, Bayan ta shiga ya ja motar suka wuce Sai da ya fitar da motan ya daidaita ta a kan kwalta, sannan ya tambaye ta inda zai bi Hannu ta sanya a Jakarta ta ciro address ɗin gidan su ta miƙa masa Amsa yayi ya duba, ya san sunan anguwan a baki, but bai san a ina ne ba tunda ba wai ya cika yawo bane shi tun usuli, Don haka yace mata, "bai san hanyar da zai bi ba amma ta riƙa nuna masa koda da hannu ne." To a haka ne har suka ƙarisa anguwan nasu, ya tsayar da motan a dai-dai lungun gidan su, After ya dakatar da motan; sai ya zuba mata ido yana kallonta kamar kar ya ɗauke ido a kanta Ita kuma murmushi tayi tare da mishi godiya da hannunta tana shirin buɗe ƙofan ta fice But tuni ya dakatar da ita wurin furta, "har yanzu ba ki bani wayan naki na gani ba? Please ki bani mu gani." Kallon fuskarsa tayi, ganin yanda ya kafe ta da kallo shiyasa tayi ƙoƙarin ciro wayan daga cikin Jakarta, zaro Jakar tayi a hammata before ta buɗe ta ciro ƴar ƙaramar wayanta da ta ji jiki ta sauya kamanni, sanadin hakan ne yasa har yanzu take tare da wayan batare da ta siyar ba, Miƙa masa tayi a kunyace ya amsa yana duba wa, murmushi kawai yayi a zuciyarsa yana furta, "Allah Sarki! Baiwar Allah, maybe sabida yanayin wayan ne yasa ta ƙi nuna min." Sai ya ɗauki wayansa da ke ajiye ya soma buɗe wa, bayan ya buɗe ya cire simcards ɗin sa tare da buɗe nata itama ya ciro Tana kallo ya sauya layin ciki ya saka nata a babban nashi, bata iya cewa komai ba har sanda ya miƙo mata wayan, amma kuma ta kasa amsa sai ma idanu da ta zuba mishi don bata fahimci mai yake nufi ba "Karɓi mana, na ba ki ne, ki yi amfani da nawa zai fi miki daɗin aiki, wannan kuma sai ki kyautar." Ya haɗa da natan ya miƙa mata, Ganin ta ƙi amsa still shiyasa yayi maganar in serious face A sanyaye ta saka hannu ta amsa wayoyin, bata da bakin magana shiyasa tayi shiru godiyar ma ta kasa mishi don bata san me zata ce ba "To zan wuce, but Insha Allah tunda na ga gida wani lokacin zanna riƙa zuwa ina ɗaukar ki kawai; since hanyar mu ɗaya ai, baza ta bani wahala ba zuwan." Kallonsa tayi suka haɗa ido, sai tayi mishi murmushi tare da ɗaga hannayenta ta soma mishi godiya Duk da shi bai fahimci mai take cewa ba amma ya gane kamar godiya ne, yace, "kar ki damu yanzu kin zama Ƙanwata, komai kike so ki yi min magana kanki tsaye, yanzu ki tafi kar a ji ki shiru sai gobe in mun haɗu." Hannu tasa ta buɗe motan, tana shirin fita ta hango Jabir ya fito lungun gidan nasu yana layi irin tafiyar nan nasa ta mashaya, da sauri ta dakata nan da nan gabanta ya faɗi, sai ta diririce lokaci guda ta mayar da ƙofan ta rufe tana zare idanu Mamaki ne ya kama Hanif ganin yanda ta ruɗe lokaci ɗaya, inda take bi da kallo ya bi da idanunsa yana kallon Jabir; da ya zo ya gibta ta wurin Motan bai ganta ba, Sai kuma ya mayar da kallonsa gare ta ganin yanda take sauke ajiyar zuciya kamar wacce tayi gudun tsere, alamun tsoro ya bayyana a tare da ita, buɗe baki yayi yace, "lafiya Amrah? Me ya faru ne?" Saurin kallonsa tayi a tsorace tana ƙanƙame jikinta, cikin yanayin da babu natsuwa a tare da ita ta soma girgiza mishi kai alamun babu komai, sai kuma ta buɗe kofan ta fice da sauri; ba tare da ta waiwaya ba ta nufi hanyar gidan nasu da ɗan saurin ta, har da haɗawa da gudu Hakan ba ƙamarin mamaki ya ba Hanif ba, duk yanda aka yi akwai wani abu da ke damun Amra, wanda ganin wannan mutumin ya haddasa mata shiga ruɗani nan take, duk ta sukurkuce babu natsuwa a tare da ita, shiru ya ɗan yi na wani lokaci ya gaza tafiya, actually har cikin zuciyarsa ya damu da ita, a ɗan kwanakin nan da tunanin ta yake kwana yake tashi, ji yake yi tamkar ya soma sonta a cikin zuciyarsa, amma har yanzu ya kasa gasgata wa, idan har sonta yake yi taya ya zai fara isar da saƙon sa gare ta? Wanne irin soyayya zasu yi tana kurma? Ta ina zai fara? Gaskiya yana matuƙar jinta a ransa koda soyayyar ne bai san ta inda zai fara ba, shiyasa ya bama kansa lokaci don ya gane shin da gaske ne soyayyarta ne a cikin zuciyarsa; ko kuma tausayi ne kawai? Duk da natsuwarta da kamun kanta su suka ja ra'ayinsa gare ta har yake iya jin wani abu a tattare da ita, tana da shiga rai ne, komai nata yayi mishi domin ba ƙaramin burge shi take yi ba, Motansa ya ja ya nufi hanyar gida ransa duk a jagule, da tunanin halin da zai shiga har ya bayyana ta a wurin Iyayensa, mai zai faru idan sun san tana da laluran rashin magana? Har yakai gida tunanin Amra ya tsaya mishi a rai Momy da Sadiq ya samu a falon suna zaune suna kallo, After ya shigo sai da ya samu wuri gefen Sadiq; before ya yi wa Momy sannu da gida, Sadiq shima yayi masa welcome back Momy bayan ta amsa take cewa, "yau SHAREEF ya bar ka da aiki, ban san meyasa yau ya ƙi zuwa ba ya wuni a daki, a tunani na bai da lafiya ne yace min lafiyarsa lau, kawai bai jin zuwa ne, Dadyn ku ma ya yi masa magana amma ya ƙi zuwa, na san maybe ya faɗa maka ko wani abun ne ke damun sa?" Kallonta yayi yace, "A'a Momy, bai sanar min ba, nima dai na zuba ido in ga ko zai zo but na ji shiru, amma na san lafiyan ce maybe gajiyan Australia ne bai huce ba." Ya ƙare maganar da ɗan murmusawa Inda Momy kuma ta taɓe baki tare da mayar da hankalin ta a kan TV, take cewa, "ta yiwu, tunda tun jiyan a haka ya dawo babu walwala, daga can ya samu matsalar sa zai juye mana shi a nan." Dariya Hanif yayi yana miƙe wa ya nufi hanyar upstairs, "Momy ina Dady ne?" "Yanzun nan ya fita wlh, ina tunanin wurin Doctor Umar ya tafi don da shi na ji suna waya." "Ok." Yace yana wuce wa saman, Ɗakin su ya nufa ya tura kofan ya shiga da sallama SHAREEF da ke kwance a saman dogon kujera, daga shi sai singlet da gajeren wando, idanunsa a rufe ya nannaɗe hannayensa a ƙirji kamar mai barci, sai dai jin sallaman Hanif ɗin ne yasa shi buɗe madaidaitan idanuwansa masu cike da damuwa; har sun kaɗa sun yi ja sabida tunanin da ya ƙwazzafi kansa dashi, Bai amsa mishi sallaman ba illa bin sa da kallo da yayi kamar yana neman wani abu a jikinsa Shi kuma zama yayi yana ajiye jakarsa tare da furta, "wash Allana! Na gaji wlh, aiki babu dad'i, shine ka ƙi zuwa ko?" Ɗauke kansa yayi yana mai mayar da idanunsa ya rufe, tare da ƙoƙarin juya kwanciyar sa ya juya mishi baya "Wai Bro baza ka cire damuwar yarinyar nan a tare da kai ba? Ban san meyasa ka damu kanka da ita ba, since ka gano wannan laifin mai girma duk da na san abun da ciwo, yanzu mataki yakamata ka ɗauka, ko rabuwa ko kuma kayi haƙuri ku ci gaba daga inda ku ka tsaya, tunda dai na san soyayyar da kake mata bazai sa ka rabu da ita ba ko?" Ya ƙare maganar da son jin mai zai faɗa Ai kuwa tuni SHAREEF ɗin ya tashi zaune yana faman kallonsa, fuskarsa cikin damuwa kamar zai yi kuka yace, "tabbas bazan iya rabuwa da Haseena ba, abun da tayi min ya matuƙar min ciwo cus ban taɓa expecting haka daga gare ta ba, amma kuma har yanzu bata kira Ni ba, ina ta zaman jiran kiran ta domin ta bani haƙuri amma shiru." Dariya Hanif yayi, "wai kana nufin sai ta baka haƙuri sannan zaka haƙura? Mene ne amfanin hakan?" Wani kallo SHAREEF ya watsa mishi before yace, "sabida girman laifin da tayi min mana, kana tunanin Ni zan bi ta duk da wannan laifin but Ni zan sake bibiyan ta? Duk da ina sonta sai na hukunta ta, wlh da zan iya rabuwa da ita da tuni na rabu da ita, domin zuciyata baza ta taɓa samun sukuni ba tunda na kama ta tana cin amanata, a ɗan wannan lokacin ji nake yi kamar zan mutu sabida baƙin cikin abun da tayi min, amma na kasa cire ta a rai, ina son Haseena! son da ba na tunanin zan iya ma wanin ta." Sai ya buga tagumi yayi shiru idanun nan sun kaɗa sun yi jazur Shiru Hanif yayi yana kallonsa, yayinda har a ransa haƙiƙa yana tausayin ɗan uwansa, wai wannan wacce irin soyayya ce? Shi a ransa sam ba ya son Haseena da SHAREEF; domin har ga Allah bai ga dacewar su ba, ya fi ganin dacewar su da Maryamu tun sanda ya soma ganin ta, ita ce zata fi dacewa da shi, ko don tausayinta da yake ji tana fama da dakon soyayyar wanda babu ita a gabansa, yana jin har abada in har akwai Haseena; tabbas bazai taɓa son Maryamu ba, Kamar yayi mishi maganar ta haka yake ji, amma kuma sai ya fasa gwara ya bar sa da abun da ke damun sa, amma shi a ganin sa mai ya rage kuma, in har ya samu Haseena da wannan cin amanar bai kamata ya ci gaba da sonta ba, tunda zina ta aikata ta ba wani kanta bayan shi, ko don wannan ya ci ace soyayyarta ta fice daga ransa, amma kuma wai zaman jiran ta ba shi haƙuri yake yi, lallai kam! SHAREEF yayi nisa ba ya jin kira. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____A cikin kwanakin nan SHAREEF ya zauna da damuwar jiran kiran Haseena kamar yanda yake hasashen zata neme shi ta ba shi haƙuri, amma abun mamakin shiru babu kiran ta Ita kuma tana can cikin wani hali a lokacin, tun mafarkin da tayi na gane-ganen mutane; yanzu kuma abun sai ya zame mata jiki, abubuwan da take gani a mafarkin ta sun soma tsorata ta, tun tana ɓoye wa sabida abun yana ɗaure mata kai, sabida yanayin mafarkin da kullum ta kwanta sai ta ga mutanen suna shan jini ana yanka mutane a zuba jinin a basu; suna sha suna waƙe-waƙe da sirkulle, a firgice take a kwanakin, ga Nana da take gani a cikin mafarkin, itama tana tare da mutanen, ita take kamo ta koyaushe ta bata jinin nan ta sha, kuma bata taɓa mata musu ba, Abun ya soma tsorata ta shiyasa ta kasa ɓoye wa ta sanar da Nanan abun da take gani a mafarkin ta Nana kuma tayi murmushi tace, "zata faɗa mata sirrin da bata sani ba a yanzu." Don haka ta zauna ta feɗe mata biri har wutsiya na sanya ta a ƙungiyar su da tayi na Secret society, a cewar ta, "sabida tana sonta da ƙaruwa, komai take so a ƙungiyar zata samu, hatta SHAREEF in har tana so ta sarrafa shi yanda take so, to wannan damar ta ne duk abun da take so zata mallake shi in har zata yi wa ƙungiya biyayya." Haseena ta ruɗe ta kiɗime da jin bayanan Nana, hankalin ta yayi matuƙar tashi wanda yasa lokaci guda ta faɗi ta sume sabida tsananin firgici da jin abun da ya fi ƙarfin ta, ƙwaƙwalwan ta ta gaza ɗaukar halin da take ciki Ita kanta Nana ta tsorata ganin yanda Haseena ta sume babu nimfashi a jikinta, amma sai ta daure ta zuba mata ruwa ta farfaɗo nan take, tana kallonta tace, "You should calm your mind, stop putting fear in your heart, nothing will happen to you, nayi haka ne don taimakon ki sabida ina sonki da ƙaruwa a cikin mu." Sai ta riƙo hannunta tana murmusawa ta ƙara da faɗin, "haba babe, na san kina son ki ji dadin rayuwa, you will be happy to find yourself among us, whatever you will get you don't have to worry, just calm down." A firgice Haseena take kallonta, idanunta har sun sauya launi tsaban tashin hankali ga hawaye sun cika mata idanu, cikin tashin hankali ɗakyar take iya maganar ma, don tsoro Nanan take bata, da sarƙewar murya tace, "No, a'a, ba na so, Ni ba na son wannan harkan, bazai yiwu ba, taya ya za ki saka Ni a cikin ƙungiya ba tare da amincewa ta ba? That may not be possible, I can't; just remove Me, I don't want to." Smile Nana tayi tace, "already na saka ki a ciki yanzu kin zama ɗaya daga cikin mu, kawai haƙuri za ki yi amma baza ki taɓa iya fita ba, If you think you can leave, there is a condition". [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE5* _____Da sauri ta haɗiye yawun tsoro; idanunta a dalale a kan Nanan ɗakyar ta furta, "for what?" Murmushi Nana tayi tace, "sharaɗin shine ba a fita a ƙungiyar mu sai dai mutuwa, in kin shiga kin shiga kenan, in kuma kina so ki fita sai dai ki mutu." Zumbur Haseena ta miƙe tsaye tana kallonta zuciyarta na luguden buga wa, tamkar zata faso ƙirjinta don tsaban tsoro da tashin hankali, gaba ɗaya babu sukuni a tare da ita, hawaye tuni sun wanke mata fuskarta tsaban tashin hankali, Wannan wacce irin mummunar ƙaddara ce ke shirin son ya tunkaro ta? Ina ta kawo kanta take kokarin kashe kanta? Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Ta kiɗime ta rasa inda zata saka kanta, hawaye kawai ke ɗiga a kan face ɗinta suna ɓulɓuluwa da sauri - da sauri Miƙe wa Nana tayi tana kallonta tace,  "You better calm down because you don't have any other chance than this, muddin kika ce za ki fita to sai dai ki rasa rayuwarki, ba ki da wani zaɓi Haseena, komai naki a tafin hannuna yake, zan iya sarrafa ki a duk sanda na so." Sai ta shafa face ɗin ta tana sakar mata killer smile, before ta wuce tabar Falon gaba ɗaya Har ta fice kallon hanyar da ta bi take yi, kamar tayi suman wucin gadi bata san me ke wakana ba a lokacin, komai nata ya tsaya cak babu sauran abun da ke motsi a tare da ita, illa hawayen da ke ɗiga har yanzu suna kwaranya a ƙasa, Sai kuma can ta zame ƙasa ta koma saman kujeran jikinta na kerma, kuka ta fashe dashi cikin tsananin tashin hankali da nadamar kasancewar ta a nan ɗin, "wayyo Allana! Mai na ja ma kaina; me ke shirin faruwa dani ne? Kungiyar asiri? Ni ɗin? Na shiga uku na lalace! Meyasa wannan ƙaddaran zata faɗo rayuwata? Meyasa na yarda da ita after all na san wace ce ita?" Kuka ta dinga yi tana sambatu gaba ɗaya ta firgice ta rasa inda zata tsoma kanta, Lokaci guda wani tashin hankalin ya riske ta saboda ganin ta da tayi a dokan taji cikin mutanen da ta saba yin mafarki da su, ciki kuwa har da Nana da su Herin ƙawayenta, Yayinda wani ƙaton Mutum mai dogon gashi yake tsaye a tsakiyar su wanda shi ya fi su munin gani, alamu shi ne babban su kuma Oga a cikin su Idanunsa jazur yake kallon inda Haseena ta sandare ta fita a hayyacinta, tsawa ya daka mata sai ga ta a gabansa a ɗaure idanunta a kafe a kansa, alamun ma ba ita take sarrafa kanta ba, wani kallo yake watsa mata tare da magana da turanci, "tunda kika kasance a cikin mu dole ki bi ƙa'ida da dokoki, daga yau kin shigo cikin mu kenan da ke zamu riƙa yin komai, ko kina so ko ba kya so, don haka daga yanzu tunanin ki mu zamu riƙa sarrafa shi, ba ke babu musu har abada." Sai ya ɗaga hannunsa take wata walƙiya ta bayyana da ƙoƙo a hannunsa, tun daga saman kanta ya soma zuba mata jinin da ke cikin ƙoƙon yana zuba jikinta, gaba ɗaya ya jiƙa ta sharkaf da jinin sannan ya ɗaga kansa ya soma sirkulle, bayan ya gama ya buga goshin ta sannan ya kamo yatsunta sai ga wasu zobuna sun bayyana a yatsun nata gaba ɗaya na hannun hagu, dukka iri ɗaya har wanda Nana ta bata su guda biyu da jima wa, Dariya ya ɓaɓɓake dashi yana kallon jama'ar da ke wurin, Nan fa suka dinga zagaye su tunda sun san me yake nufi, suna yi suna wasu karatu da babu kan gado, sun jima a haka before su dakata, kowanne cikin su ya zo yana shafa hannunta tare da mata maraba da zuwa cikin su Haseena dai tana kallonsu da jin su batare da ta gane komai ba, kuma babu damar musu bare daukar mataki, a lokacin ma jin ta take yi wani iri kamar ana sauya ta, ta kasa ƙwaƙƙwaran motsi bare ta san me ke faruwa da ita, tunda aka ɗaɗɗaka mata wani abu a baki daga nan bata sake sanin inda take ba, Sai buɗe ido tayi ta ganta a saman gadon ta cikin halin ciwo ba ta iya sarrafa komai nata Nana na gefen ta don ita take kula da ita, ganin ta farfaɗo ba ƙaramin farin ciki tayi ba, kiran sunan ta tayi tana kamo hannunta While Haseena ta amsa mata tana kallonta cikin wani irin yanayi, baza ta iya cewa ga abun da ke damunta ba amma ji take yi kamar an sauya ta "Sorry na san kina wani hali a yanzu, but bari ki yi wanka sai ki sha magani za ki wartsake ko?" Ta ƙare da mata murmushinta wanda ba ya gushe wa a kan face ɗin ta, taimaka mata tayi ta tayar da ita takai ta har cikin toilet, A takaice ita tayi mata wankan; ta nannaɗo ta a cin towel ta dawo da ita ta kwantar da ita, Sannan ta je ta zuba mata indomie da ta dafa mata ta kawo mata ta bata da kanta, sai da ta gama sannan ta ɗauko mata kayanta ta saka, A hankali ta kama hannunta tana kallonta tace, "na san za ki ji sauyin yanayi a tare da ke, kar ki damu a hankali za ki saba kina jina?" Kai Haseena ta gyaɗa mata ba tare da musu ba, saboda a yanzu jinta take yi komai take so zata iya mata babu wata gardama, jinta take yi tana son wani abu amma ta rasa mene ne Kamar Nana ta sani sai ta ɗauko mata cup da ke ajiye, wanda akwai jini ne a ciki don shine abun shan su, basu da drinks sai shi, miƙa mata tayi ta karɓa Sai da ta leƙa cup ɗin; ta ga abun da ke ciki sannan ta kalli Nana tace, "mene ne shi?" Murmushi tayi mata tace, "ki sha zan faɗa miki." Kanta ta gyaɗa mata, sannan ta buɗe baki ta kafa kai a ciki; sai da ta shanye before ta cire tana lanɗe baki kamar wata mayya Hannunta ta ɗaura a nata tace, "daga yanzu irin wannan abun shine abun shan ki, ƙarfin ki da kuzarin ki zai ninku fiye da haka, jinin wasu mutane ne da muka sha, in kina buƙata kawai kina ɗaukar cup za ki ganshi a ciki." Shiru Haseena tayi bata ce komai ba, kuma babu wani tunani a ranta face kallon Nanan da take yi "I will explain to you everything that is in our group, you will understand everything, even the rules in it". *** Tun daga lokacin Haseena bata sake tuna SHAREEF a cikin rayuwarta ba, domin a halin da take ciki komai nata ya sauya ta tsinci kanta a cikin wani irin rayuwa da bata taɓa tunanin ganinta a ciki ba, duniya ta soma sauya mata lokaci guda ta soma ganin sauyi a tare da ita, Kuma a ɗan ƙanƙanin lokaci ta fahimci kungiyar su wanda har itama an bata dama tana gudanar da tsafi, komai ta taɓa in tana buƙatar abu zata iya samu, musamman ma kuɗi lokaci guda ta jiƙe da kuɗi, basu da sana'a sai fita yawo da su Nana suyi abun da suke so, Ba iya SHAREEF ba har Iyayenta ta soma manta wa da su a rayuwarta; since bata da time ɗin su Kusan satin ta uku cif da kasancewar ta a cikin ƙungiyar, wanda SHAREEF ya gaza jure rashin ta duk da fushin da ya ɗauka da ita, jin shiru bata neme shi ba dole shi ya ɗauki waya ya kira ta, Sai lokacin ta tuna dashi, kuma ta tuna abun da ya faru a tsakanin su before ya tafi ya barta, har yanzu tana son SHAREEF soyayyarsa bata sauya a tare da ita ba, Amma kuma babu sha'awarsa a tare da ita don Nana ta ɗauke mata wannan; ita kaɗai take jin sha'awarta, in har ba da ita zata yi harka ba to baza ta taɓa bukatar wani ba, Lokacin da ta ɗauki wayan suna magana bata nuna masa komai ba, illa ma cewa da tayi, "ya manta da ita bai neme ta ba tsawon wannan lokacin, sabida ya dena sonta ko?" SHAREEF ya rasa ma mai zai ce mata jin abun da tace, sai yayi shiru yana jan numfashi tare da jinjina ƙarfin halin ta "Wai dear nayi magana kayi min shiru, meyasa ka rabu da Ni ne sai wannan lokacin zaka kira Ni? Nayi fushi da kai since ka dena sona, shikenan." Sai ta kashe wayan ɗib Tsantsan mamakin abun da tayi masa ne yasa shi kallon wayan; yayi kasaƙe yana kallon phone ɗin, lokaci ɗaya ya soma jin ransa na ɓaci saboda abun da tayi masa, yanzu ya sake tabbatar wa dole akwai wani a gabanta Haseena ta soma gajiya dashi, dialing numban ta ya soma yi ransa na ƙuna, yana jin ta ɗauka ya soma magana cikin zafi, "Haseena, Ni zan kira ki ki kashe min waya? Bayan duk wannan laifin da kika yi min? but now I called you and you hung up on me? Me ke damun ki?" "Me ka gani? Ko nace maka wani abun na damuna ne? Kai ka tafi ka bar Ni a kan laifin da ban aikata ba, SHAREEF kai kaɗai ne wanda nake so ban taɓa kusantar wani mahaluki ba sai kai, meyasa ka kasa ganewa ne?" "Haseena, Ni kike yi wa tsawa haka?" Yayi maganar cikin tsananin mamaki da al'ajabi Shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya, yayinda ta zuba wa Nana idanu tana kallonta kamar yanda itama take kallonta tun shigowar ta cikin ɗakin SHAREEF kuma daga can kashe wayan yayi batare da ya furta komai ba saboda yanda ransa yayi matukar ɓaci Kallon wayan take yi tayi shiru tana tunani a ranta Nana zama tayi gefenta tana sanya hannu ta soma shafa ta before tace, "babe, me ke faruwa ne? Da ke da Boyfriend naki ne ko?" Ɗago kai Haseena tayi tana kallonta; but still ta ƙi yin magana "Wai meyasa baza ki rabu da shi bane? Ni fa ina kishin ki a kan wannan mutumin sabida na ga alamun kina matuƙar ƙaunarsa, har yanzu na kasa cin galaba wajen raba ku, yanzu ba amfanin da zai miki ki rabu dashi Please?" Girgiza kanta Haseena tayi tace, "ke ba ki san irin ƙaunar da nake mishi ba, bazan iya rabuwa dashi ba, SHAREEF wani ɓangare ne na jikina, koma in ce ya zama jinin jikina, bazan iya rabuwa dashi ba, nawa ne shi Ni kaɗai, kuma bazan taɓa bari wata ta same shi ba bayan ni, ina da auren sa a kaina yanzu kinga dole in ɗauke sa ya dawo gare Ni na har abada, ina son ya so ni Ni kaɗai ya manta ɓacin ran da na sanya mishi, zan iya aikata hakan ko?" Wani kallo Nana ta watsa mata da cewa, "No bazai yiwu ba, domin akwai sharaɗi a tsakanin mu, Haseena, you still don't know how much I love you, right? Idan ya dawo gare ki zai yi mana katanga a tsakani, don haka bamu buƙatar sa a nan, ki manta da zancen sa in har soyayyarki ce ke kaɗai ce a zuciyarsa, daga ke bazai sake son wata Mace ba bayan ke, zuciyarsa zamu mallaka, kuma duk abun da kike so shi zai yi miki babu gardama, bazai sake miki musu ba ko ya ga laifin ki." Murmushi Haseena tayi tace, "yeah, ina son haka, Of course, if you do this to me, you're done for me. ina son in mallake shi gaba ɗaya ko aina yake bazai so wata Mace ba bayan Ni, domin shi nawa ne, ina sonsa da gaskiya, rasa sa kamar na rasa raina ne." "Kar ki damu babyna, ki bamu lokaci komai zai sauya, kar ki sake damuwa dashi zai biyo ki duk inda kike so, yanzu lokacina ne, ki shirya mu fita We will meet them Herin, there is a party to go to." Then they got up and went into the bath together, bayan sun shirya suka fita a motan Nana. *** _____Gaba ɗaya SHAREEF ji yake yi zuciyarsa na masa zafi da abun da Haseena tayi masa, tabbas Haseena ta dena sonshi yanzu, har shi zai kira wayanta but basu gama magana ba ta kashe? Abun da bata taɓa masa bane, and shima ya kashe bata biyo baya ba, ransa yayi ƙololuwar ɓaci wanda yasa ya kasa ci gaba da aikin, illa ma ɗaura kansa da yayi a saman teburin yana sauke numfashi a kai-a kai, tun ba yau ba ya kula Haseena ta sauya masa, meyasa to? Me yayi mata? And ita ce ma tayi masa laifi amma take ƙoƙarin ɗaura masa laifin; tare da nuna kamar ba abun da ya faru, wane ne wannan a cikin rayuwarta? Tabbas in ya gano wane ne sai yayi masa mummunar hukunci tunda har yayi ƙoƙarin shiga tsakanin sa da farin cikin sa Tsawon lokaci ya kasa yin komai sai saƙe-saƙe da yake yi a cikin ransa, kansa ya ɗauki zafi da tunani, ji yake yi tamkar ya dauki waya ya kira ta but ya kasa, ba ƙaramin fushi yayi da ita ba amma zuciyarsa na azalzalan sa, kuma idan yace zai sake kiranta wlh sai ya ɓata mata ranta, shi kuma ba haka yake so ba, a duniya abun da ya tsana shine ya ɓata wa Haseena rai, domin ji yake yi sai ya fi ta shiga tashin hankali da damuwa, Allah ya ɗaura masa soyayyarta da bai san ya zai yi da rayuwarsa ba in ta guje sa Yana nan kwance da kai a table, har PA ya zo ya sanar mishi lokacin tashi yayi, amma ya kasa tashi, ƙarshe da ya dame shi sai ya daka masa tsawa a kan, "ya bar sa." Jiki na rawa PA ya fice yana rufo masa ƙofa, Amma bai tafi ba tunda ya san dole shi zai rufe office ɗin, Yana nan a zagaye a wurin har Hanif ya zo shiga office ɗin, Suka gaisa yana tambayarsa SHAREEF ɗin? "Yana ciki sir bai fito ba." "Ok." Yace dashi yana duba agogon hannunsa, tare da nufan office din ya shige, A yanda PA ya bar sa a haka shima ya zo ya tarar da shi, Da mamaki yake duban sa don ya san babu lafiya tunda ya gansa a haka, bai ma samu zama ba ya soma tambayarsa da lafiya? Sai lokacin SHAREEF ya ɗago kai yana duban sa, duba ɗaya yayi masa ya ɗauke idanunsa a kansa Shi kuma Hanif hakan ya ƙara saka shi a ruɗani sabida ganin yanayin idanuwansa da suka canza launi, shiyasa da sauri ya sake tambayarsa yana cewa, "wai lafiya Bro, me ya faru ne?" Haɗa kayansa ya soma yi bai amsa mishi ba, don yadda zuciyarsa take zafi da tuƙuƙi ba ya jin zai iya buɗe baki yayi magana "Don Allah ka faɗa min mai ke faruwa ne? Ka saka Ni cikin wani yanayi sabida halin da na ganka, Please Bro tell what's wrong?" "Bai da wani amfani sanar da kai. Mu je kawai." Jin hakan ya san cewa bazai faɗa mishi ba in har a yanzu ne, sai lokacin da ya mula don kansa, That's why bai takura masa ba ya miƙe suka fita a tare, A Mota ɗaya suka zo tunda yawanci hakan suke yi gaskiya, dole in har tare zasu zo Motan Hanif zai shiga ya tuƙa su, don shi bazai yi tuƙi ba, Kai tsaye gida suka nufa babu mai magana a cikin su, kowa da abun da ya dame sa. [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE6* _____Tun daga ranan SHAREEF ya so ya share Haseena daga ransa har sai ta kira sa don kanta, tunda da ita yake kwana da ita yake tashi amma tsaban haushin ta da baƙin cikin abun da tayi masa; shiyasa shima ya so ya share ta gaba daya har sai ta gane kuskuren ta, Amma inaa; abu kamar wasa zuciyarsa ta kasa sukuni da tunaninta, ga wani irin azalzala da take mishi a kanta, wani irin sabon ƙaunarta yake ji wanda yana jin ko me tayi masa bazai iya fushi da ita ba tsawon lokaci, dole ya ɗauki waya ya kira ta don kansa, kuma a ƙarshe shi ya ƙare da bata haƙuri, Don yanda take mishi shan ƙamshi tana nuna alamun tayi fushi, duk ya rikice kamar zai yi kuka don yanda ya shiga damuwa, ɗakyar ya shawo kanta don har so yayi ya je Austaraliyan amma ta hana sa Dama tayi haka ne don ta gwada irin yanda suka kama zuciyarsa kamar yanda ta sha alwashin mallakar sa, yanzu ta gane SHAREEF ya zama nata gaba ɗaya, bata da wata matsala kuma shiyasa suka ɗaura da soyayyarsu kamar yanda suka saba Yanda SHAREEF yake jin Haseena a ransa komai zai iya yi sabida ita, abubuwan da suka faru tuni ya manta da komai sai zallan ƙaunarta a rai, ba shi da aiki sai waya da ita ko video calls, a yanda SHAREEF yake matuƙar buƙatar Matarsa a kusa but hakan ya gagara, domin duk sanda ya nuna zai je wurin ta ba ta yarda, ga shi ba ya son ɓacin ranta ko kaɗan, Sun ɗauki tsawon lokaci yana magiyan tabar sa ya zo, Sai da ta mula sannan ta amince masa, domin a wurin ta zuwan nasa bai da amfani tunda ba abin da zai tsinana mata sai takura, Ilai kuwa hakan ce ta kasance, duk yanda SHAREEF ya so da samun biyan buƙatar sa a wurin Haseena abun ya faskara, kusan kuka yayi mata a ranan a kan ta amince masa, amma ta ƙi, don kwata-kwata bata da sha'awarsa ko kaɗan, idan ma yana naniƙe mata mugun haushin sa take ji kamar ta kashe shi haka take ji, but idan yana nesa sai ta ji tarin ƙaunarsa, sam ta ƙi basa haɗin kai ko ɗan romancing ɗin da yake samu ya ji dad'i wannan karon bai samu ba, tunda shi kaɗai yake kiɗan sa yake rawansa ba ta taya sa, Amma babu yanda zai yi tunda already yanda yake jin ta a rai bazai iya ganin ɓacin ranta ba, Haka nan ya dawo ƙasar babu biyan buƙata, sai na ciwo da ya kwaso wa kansa, A taƙaice dai; dole ya nemi magani a asibiti ya soma amfani dashi tunda bazai iya zama da cuta yana wahalar da kansa ba, wacce kuma yake so da ƙauna ta hana sa abun da yake so, Shi yasa duk a kwanakin SHAREEF bai da wani natsuwa ya rame sabida damuwar da ke tare dashi Hanif ne kaɗai ya san halin da yake ciki tunda shi suke kwana tare, already bai ɓoye mishi komai ba duk abun da ke faruwa ya sani, abun yana baƙanta masa rai a yanda ya ga SHAREEF ɗin ya mutu a ƙaunar Haseena, amma take wahalar da shi ba ta son farin cikin sa, ya sha faɗa masa, "idan da tana son farin cikinsa kuma tana ƙaunarsa; ko mene ne zata iya yi don ta faranta mishi, amma abun da ba haramci zasu aikata ba since ta zama Matarsa, amma take masa wulaƙanci a kai, don haka idan ma zai farka daga wannan barcin nasa da bai da amfani; yana liƙe mata babu biyan buƙata, gwara ya farka ya san inda ya dafa, shi a ganinsa Haseena ba ta ƙaunarsa wlh, idan kuma ba haka ba zai iya kashe kansa a banza a hofi tunda yana zaune da lalura yana biye mata ya kasa amsar haƙƙinsa." Idan yana wannan maganar kallonsa kawai SHAREEF yake yi, idan ma ya cika sa da zancen sai ya nuna rashin kyautawar sa a kan abun da yake faɗa, domin shi a ganinsa Haseena tana sonsa tana ƙaunarsa, don bata ba shi hakkinsa ba; ba hakan shi zai nuna ba ta sonshi ba, ya san cewa wata rana komai zai wuce da zaran ta gama karatun ta Murmushin takaici Hanif yake yi, yace, "wlh ko ka so ko kar ka so yarinyar nan ba ta tausaya maka Bro, gwara ka nemi mafita tunda ba ita kaɗai bace Mace a duniya, in fact ma ba ita kaɗai kake aure ba a yanzu, Maryam zata yi maka amfani before ka kashe kanka." "Hanif, ka dena min maganar yarinyar can, har abada ba ta gabana kuma bazan taɓa jin sonta ba bare har in ji sha'awarta, don haka kana wahalar da bakin ka ne, Haseena kaɗai nake so kuma ita ce a zuciyata, zan ci gaba da lallaɓa wa a haka ina shan magani komai zai wuce very soon." To jin wannan maganar nasa shiyasa shima Hanif ɗin ya ƙyale sa, tunda a yanda yake gani SHAREEF bazai taɓa fahimta ba, already ya yi nisa ba ya jin kira. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____Koda aka yi hutun second time; Maryamu bata dawo gida ba, a can Abuja tayi hutun ta, since Momy tace, "gwara ta zauna a can kawai tunda suna zuwa koyon computer, idan ta dawo kuma babu amfani." Hakan ne yasa Ammee bata bar ta ta dawo ba tunda ga abun da Momy tace, Ita kuma Maryamun bata damu ba, duk da ta so ta koma hutun domin a can Zaria ta fi so tayi, ba ta son ma zamanta a Kano ko don SHAREEF, since ba ta son abun da zai sa ta tuna shi a rayuwa bare ta famo gyambon da ta daɗe da warkar dashi a zuciya, Tayi zamanta a can har suka ƙare hutun suka koma school After sun yi hutun third time, dayake hutun da yawa shiyasa ta koma gida, Ammee driver ta sanya ya kawo Maryamu har Kano Ba ƙaramin farin ciki Momy tayi ba saboda ganin yanda ƴarta ta sauya gaba ɗaya, kamar ba ita ba har ɗan wani ƙiba ta kara, dama Maryamu ba baya ba wajen Kyawun jiki, sam bata da rama, sai ga shi ta samu hutu yanda jikinta ke buƙata; ta zama ƴar lukuta da ita har ɗan tsawo ta ƙara Abun da su Hanif suke tsokanarta dashi kenan, don su kansu sun sha mamakin ganin yanda tayi tsawo kamar ba ita ba, tayi fresh abun ta, sai tsokanarta suke yi Ita kuma ba abun da take yi sai murmushi, har ranta ta ji daɗin yanda suke nuna sha'awarta da ganin sauyawan ta, dama hakan take so, bare ita akwai iyayi da ficchi, tana son a yabe ta musamman yadda ta saka a ranta zata ba SHAREEF mamaki, sam-sam bata damu ta gansa ba don bata buƙatar tozali dashi, shiyasa tayi farin ciki da ta ji labarin ba ya ƙasar ma a wurin Sadiq, kwana ɗaya kenan da tafiyarsa wurin Haseena, kuma Sadiq ya faɗa mata, "gobe ne zai dawo." Shi yasa ta damu Momy, "zuwa gobe tana son ta wuce Zaria." Momy ta so hana wa, amma Dady yace, "gwara ta tafi kawai tayi musu hutun a can, daga can ma sai ta wuce, since tun sanda ta zo bata koma ba gwara ta tafi zasu ji dad'i Iyayen nata." Maryamu kuwa sai murna da farin ciki, tare da Sadiq zasu je but shi a ranan zai dawo in ya kaita, shiyasa suka shirya tafiyan da sassafe Washe gari suka wuce Zaria, gidan Iya Samira suka sauka, tunda dama sun san da zuwan su domin Dady ya kira ya fada musu, shiyasa tuni Iya Samira tayi musu girki Maryamu farin cikin ta ba ya ɓoyuwa yau ga ta a garin su ta zo gida, a guje ta rungume Iya Samira kamar zata ka da ita don murna Itama farin cikin yasa ta ƙanƙame ta tana cewa, "oyoyo.. oyoyo yau ga Meramun mu ta zo, Oyoyo Meramun Iya." Sai dariya suke yi suna rungume da juna sun ƙi sakin junan su, while Sadiq da ke gefe ya tsaya yana kallonsu shima yana dariyan, yace, "Iya wai ita kadai kika gani ne ban dani? Ko dai in juya ne?" "Haba Sadiqu taya zaka juya kuma? Ai bazan so haka ba, yi hakuri murnan ganin Meramu ne ya ruɗa Ni, ku taho mu je ɗaki." Tana riƙe da Maryamu suka shiga ciki, Bayan sun zauna take tambayarsu iyayen nasu? "Suna nan lafiya, sun ce a gaishe ki da kyau da kyau, ai ni a yau ma zan koma ba kwana zan yi ba, na dai kawo Maryam ne." "Haba dai a yau kuma Sadiqu? Ai ka bari ka huta ko? Ko zuwa gobe ne mu ɗan yi hiran yaushe gamo." Dariya yayi yace, "ai Ni ban zo da shirin kwana ba Iya, yau zan tafi Insha Allahu." Maryamu da ta tashi ta je ta ɗauko furan da ta gani ajiye, sai ta zo ta zauna tana kwankwaɗa, sai da ta ji ya ishe ta sannan ta cire baki tana hamdala, tare da furta, "Iya ki kyale sa, kawo Ni kawai yayi, kuma suna da school ya kusa kammala karatu ba damar yayi fashi." "To alhamdulillah, Allah ya dafa muku, bari in kawo muku abinci don na ga kamar da yunwa a tare da ku; tunda ga Maryamu nan har ta soma kwankwaɗe min fura, ga shi nan fa har girma kika ƙara." Dariya suka yi gaba ɗaya, While Sadiq yana cewa, "ashe kema kin gani Iya? Wlh kuwa ta ƙara girma sosai har tsawo fa ta ƙara ashe da sauran tsawon ta." "Yo ai dole ne duk wanda ya ga Maryamu ya san cewa ta sauya, musamman mu da muka daɗe bamu ganta ba, zaman can ya amshe ta ina tunanin Jikana SHAREEFU ya iya kiwo, har fa ajiye kumatu tayi; ka duba ka gani." Sai dariya Sadiq yake yi yana cewa, "ƙwarai kuwa Iya, ga su nan kamar burodi." Ita kuma Maryamu taɓe baki tayi jin an ambaci SHAREEF, yayinda ta sauya zancen da faɗin, "ita barci take ji ma, ba ta bukatar komai yanzu sai ta tashi." Iya tace, "ta hau gadonta ta kwanta to, bari ta kawo ma Sadiq abincin ya ci." "Nima Iya ba wani ci zan yi ba, amma kawo in sa albarka ko kaɗan ne." "Yauwa Mijin, amma ai bazan ji dad'i ba har ka tafi baka ci abincin Matarka ba, gani zan yi kamar ban iya ba tunda ka ƙi ka yaba." Ta miƙe ta nufi inda ta ajiye coolan abincin; ta ɗauko ta dawo dashi ta zuba mishi, Yana ci suna hira cikin raha da dariya Maryamu kuwa tuni barci ya soma fizgarta, tun tana jiyo dararrakun su da hiran su sama-sama; har dai ta dena ji barci ya ɗauke ta Sai da aka kira sallan azahar sannan Sadiq ya fita ya je yayi ya dawo, Shima sai ya ɗan kishingiɗa tunda Iya Samira ta matsa mishi ya kwanta ya huta before ya tafi, Shi yasa shima ya kwanta babu jima wa barci ya ɗauke sa Sai karfe huɗu Iya Samira ta tashe su gaba ɗaya, Bayan sun yi sallah sannan Sadiq yace, "zai wuce." Tare suka fita har Iya Samira ta raka su Babban gidan su suka gaisa da jama'a sannan suka fito, Sadiq ya hau mota ya tafi bayan sun yi sallama Maryamu sai ɗaga mishi hannu take yi, har sai da ta ga ƙulewar sa sannan ta bi bayan Iya Samira da tuni ta shige gida. *** _____Kwana biyu Maryamu tayi a wurin Iya Samira; ta wuce ƙauyen su, suma kwanaki biyun da tayi; tayi su ne tamkar a ƙaya, don Allah -Allah take yi ta ganta a ƙauyen su wurin Iyayenta, Babu yanda Iya Samira ta iya dole ta barta ta tafi, A cewarta, "zata sake dawowa tunda hutun nata da yawa, ba yanzu zata tafi ba." Su kansu su Inna bakin su ya ƙi rufuwa da suka ga Maryamu, yanda ta sauya musu a fuska sai abun ya basu sha'awa "Ikon Allah! Ashe da rabon za ki ƙara tsawo Maryamu, kinga yanda kika girma kamar ba ke ba? Anya ba taliyan birni kike ci ba ya ƙara miki tsawon ƙafa? wannan ma ƙiris ya rage ki kamo Ummita wlh." A cewar Umma Jummai tana kama haɓa gunun mamaki Ban da dariya ba abun da Maryamu take yi Inna ma tace, "wlh nima abun da na gani kenan, har kumatu ta ƙara tayi ƙiba abun ta, ashe dai zata yi ƙiba." "To ai kin san ita tun farko babu rama a jikinta, amma Ni kaina ban yi zaton zata yi jiki haka ba, ikon Allah! Kuma kinga duk ƴan gidan babu mai jikin Maryamu, ta fita daban dai kawai." Umma Jummai ta sake furta hakan tana miƙe wa ta fita a ɗakin, Tare da cewa, "bari in kawo miki abinci ki ci kafin Baban naku ya dawo, kinga gidan ma shiru babu kowa." Maryamu tace, "ai Umma ki bar shi kawai, gidan su Aunty Ummita zan fara zuwa, in je in zagaya su don dasu nake kwana musamman Bintu rabin raina, nayi kewarta wlh, bari in je in ga gida." Inna tace, "dama mai hali ba ya fasa wa, daga zuwa za ki soma bin gidaje baza ki bari ki huta ba?" Tura baki tayi tace, "kai Inna! Wlh na sauya sosai, nayi kewarsu ne gwara in fara zuwa in gansu." Ta miƙe tana ɗaukar gyalen ta tare da ficewa Umma da ke wajen kichen, take kallonta da faɗin, "to ai ba ki san gidan Bintun ba, sai dai in kin je ki saka Yaran Ummitan ko Indo su nuna miki, Allah ya kiyaye hanya kar ki jima fa kinga Magriba ta gabato, yanzu za ki ga Babanku ya dawo." Amsa mata tayi tana yafa gyalen ta, tare da ɗaura igiyar takalmanta da ta zura su masu shegen tsini kamar yanda ta saba, tayi musu sallama ta fice tana tafiya cikin yanga da ƙwalisa, Dama an samu abun da ake so ne, bare an zo ƙauye shiyasa iyayin nata ya ƙaru; tafiya ma kansa ɗakyar take yi kamar baza ta taka ƙasa ba, duk inda ta wuce kuwa sai an kalle ta, wasu kuwa ba sa gane ta sai tayi musu magana don iyayi su san ita ce, suyi ta mamakin wai Maryamu ne haka ta koma ƴar gayu? Sai su saki baki suna bin ta da kallo kamar wacce ta sauya musu, To hakan ne ma don gani suke yi kamar ba ita ba, abun ka da baƙauye haka labarin ya soma bazuwa nan da nan ana maganar Maryamun, Ita dai tuni ta wuce gidan Indo don nan ta fara zuwa Dayake sun san da zuwan nata tunda sun san tana garin, amma basu san cewa ta zo ƙauyen ba, shiyasa Indo ta sha mamakin ganinta a yanzu din, tace, "kai Maryamu, ke ce haka?" Dariya tayi tana cewa, "wlh kuwa Aunty, zuwana kenan nace bazan zauna ba bari in je mu gaisa." "To shiga ciki, bari in kwashe ruwan nan don Allah in zo." Wuce wa Maryamu tayi ta shiga ɗakin Indo, wanda sasan ta daban ne da sauran mutanen gidan, babu Yaran ma a gidan shiyasa Maryamu ta ɗaga murya tana cewa, "halan Yaran ba sa nan ne?" "Eh wlh suna islamiyya, Salim kuma yana gareji sai dare zasu shigo da Babansu." "Wai Aunty har ya fara zuwa gareji ne?" "Wlh kuwa, to ya ƙi makarantar ba ya son islamiyya, shiyasa Babansu yace gwara ya riƙa bin sa tunda karatun ne bai so, wai shi yayi girma kin san halin Yaran nan Maza, da zaran sun yi tsawon ƙafa sai ki ga suna gudun Islamiyya." Ta ƙare maganar tana shigowa cikin ɗakin; tare da share hannunta jikin zanin ta, Zuwa tayi ta zauna a gefen Maryamu tana kallonta cike da fara'a, "wai Maryamu haka kika sauya? Ko dai mun samu ƙaruwa ne?" Waro ido Maryamu tayi tace, "kamar ya Aunty?" Indo kuma hararanta tayi tace, "ban sani ba, ai kin san me nake nufi; ko har yanzu halin nan naki na nan na rainin wayon?" Dariya ta kwashe dashi tace, "kai Aunty, wlh ban gane me kike nufi ba, yo na san meye ƙaruwan da kike magana a kai?" "To ciki nake nufi, tunda na ga kin sauya ɗin nan kin yi kumatu alamu ya nuna mun samu ƙaruwa ne." Maryamu baki ta hangame da ƙarfi tace, "tab ɗijam! Wanne ƙaruwa Aunty? Wa ya faɗa miki a gidan Miji nake? Ina fa Abuja ina zaune a can nake karatu na." "Ke don Allah? Faɗa min gaskiya?" "Wlh kuwa Aunty, Ni ina Abuja ina karatu wurin ƙanwar Momy, babu wani ciki a jikina zaman dad'i ne kawai da Hutu shiyasa kika ga na ajiye tumbi; in ma wannan kike magana." Ta ƙare maganar tana shafa cikin ta tana bushe wa da dariya Bugun ta Indo tayi tana dariyan itama, tace, "Maryamu kenan! Baki ya san daɗi an samu abun da ake so, har yanzu hali na nan, wlh mun yi kewar ki, kuma hutun sai ya amshe ki sosai, gaskiya ba ƙaramin kyau kika yi ba, har fa wannan baƙin da kika fi mu duk ya shige kin yi fresh abun ki." Tura baki tayi gaba tace, "kai Aunty! Aina na fi ku baƙin? Wlh ban fi ku ba." "Ai sai ki yi, kowa ya san kin fi mu baƙi, baƙin ki kamar gawayi, Allah ina ganin Shatima ne kawai ya biyo ki amma kaf gidan mu kin fi mu baƙi." Ta ƙare da dariya; tunda dama tayi ne don tsokana Ilai kuwa Maryamu tuni ta ɓata fuska, don a rayuwa ta tsani su ce mata ta fi su baƙi, kaf gidan ita ce baƙa Sai da ta ga ta soma kumbura fuska shiyasa ta koma rarrashinta tana faɗa mata, "da wasa take yi." Haka dai suka ci gaba da hiran nasu gunun ban sha'awa, Tana shirin ma tafiya ne Ummita ta zo gidan, since ta ji labarin zuwan nata shiyasa ta tafi gida aka ce mata Maryamun ta fita zuwa gidajen su, Maimakon ta wuce gida sai ta biyo ta gidan Indo don ta san baza ta wuce gidan ba ƙila, ko kuma gidan Bintu, ta fi gasgata dai ƙila tana gidan Bintu, amma bata wuce ba tace bari ta soma duba gidan Indo tunda nan ne kusa, Ai kuwa tana shigowa ta tarar da ita, "Dama kamar na sani, nace bari in fara shigowa nan ko Allah zai sa in ganki, ashe kina nan?" Tashi Maryamu tayi ta rungume Ummita kamar zata ka da ita don murna Sai da tayi da gaske ta ture ta tana cewa, "ban san sakarci fa, meye haka kamar ba ki girma ba?" "Allah murnan ganin ki nake yi Aunty, dama yanzu zan wuce muje gidan naki." Indo na dariya tace, "kinga yanda Meramun Bashir ta canza tayi kumatu ko? Kamar ba ita ba." Ummita ta kama haɓa tana kallon Maryamu da ke ta wangale baki, kallon sama da ƙasa tukunna tace, "abun da na gani kenan na kasa magana, Allah mai iko! Kamar ba ita ba wlh, rayuwa kenan!" Haka dai suka dinga maganganu suna tsokanar Maryamun sai dariya take musu, don ita farin cikin ganin ƴan uwanta ya fi mata komai a wannan gaɓar, ba ƙaramin kewar su tayi ba, ƙarshe ma a nan suka zauna basu tafi ba har Yaran Indo suka dawo suma sai faman murnan ganin Maryamu suke yi, Haka ta tasa su gaba ta buge wannan ta mangare wancan tana cewa, "sun ƙara ƙaton kai na rashin ji." Sai da aka kira Magriba sannan suka fita, Ummita zata wuce gida ita kuma Maryamun zata wuce gidan Bintu, Tace mata, "ta nuna mata gidan Bintu can zata tafi." Ummita tace, "kawai ta haƙura zuwa gobe sai ta je, tunda yanzu Magriba tayi gwara ta koma gida." But Maryamu ta ƙi, a cewarta, "tana son zuwa yau, ko ba jima wa zata yi ba gobe zata sake koma wa, baza ta iya kwana bata ga Bintu ba zata iya mafarki, tunda ga baki ga hanci wlh sai ta je zata samu sukuni." Duk yadda Ummita ta so ta hana ta don ta koma gida, amma ta ƙiya, shiyasa tayi mata kwatancen gidan; since babu nisa da gidan Kakannin su. [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE7* _____Lokacin da Maryamu ta je gidan Bintu, Mijinta ya dawo a time ɗin, shi ne ma a waje yana ƙoƙarin yin alwala ya fita, Bintu ta shiga ɗaki ɗauko masa hulan sa, sai jin sallaman Maryamu tayi, duk da bata yi tunanin ita bace amsa sallaman kawai tayi AbdulHadi da ke faman kuskure baki, bai kai ga amsa sallaman nata ba tunda ya saka ruwa a baki, yana bin ta da kallo da mamakin ganin ta ya tofar da ruwan yana cewa, "kamar Maryamu nake gani?" "Ni ce, ba kama ba." "Ikon Allah! Yaushe a garin?" "Yau, ina Bintu take?" "Bintu... Bintu." Ya soma kwaɗa mata kira da saurin sa Amsa mishi tayi tana fitowa rike da hulan, amma ganin Maryamu a tsaye tana kallonta da dariya a kan face ɗin ta, sai ta washe baki ta kwatsa ihun murna tana kiran sunan ta, A guje kuma ta nufe ta; ba tare da ta damu da ɗan cikin da ke jikinta ba, wanda tuni ya fito ana ganin sa, ta nufe ta ta rungume ta tana ihun murna Itama Maryamun farin ciki take yi tare da ƙanƙame ta suna tsalle a tare AbdulHadi na tsaye yana washe baki yana kallonsu, sai dariya yake musu ganin yanda suka ƙi sakin juna, wannan ta kira sunan wannan; wannan ta kira sunan wancan, Sai da ya ga sun saki juna yake mata sannu da zuwa tare da tambayarta hanya? Bayan sun gaisa sai ya ci gaba da alwalan sabida an kusa shiga Masallaci, Su kuma suka shiga cikin daki Maryamu sai kallon Bintu take yi tana kama haɓa, can kuma sai ta tuntsire da dariya tace, "ikon Allah! Wai dama ciki kike dashi Bintu babu labari? Sai da na zo na gani?" Hararanta Bintu tayi tace, "to ya son ranki?" "Raina sakayau wlh, gaskiya nayi farin cikin ganin ki a haka, ki ce babu jimawa zan sake dawowa suna, don wlh nayi farin cikin ganin wannan cikin ba kaɗan ba." Murmushi kawai Bintu tayi tana kallon Maryamun gunun sha'awa, sai ta miƙe ta ɗauko mata ruwa a kofi tana ajiye mata, tare da furta, "wai yaushe kika shigo kauyen ne? Nima fa sai jiya na ji labari a wurin Shatima da ya zo gidan nan, yake faɗa min kina gidan Iya Samira kin kusa zuwa, wlh na zata ƙarya ne sai da na tambayi Aunty Ummita." "Tab! Ai kwana na biyu a can wurin ta, na matsu ne in zo shiyasa na gudo na ƙi zama, amma zan jima ai tunda a nan zan yi Hutu, zan koma can ma." Tayi maganar tana ɗaukar ruwan tare da ƙoƙarin sha, sai kuma ta tsaya tana duba wa before ta ajiye tana taɓe baki Bintu da ke faman kallonta tace, "lafiya?" "Babu komai, kinga ba fa dadewa zan yi ba sabida dare ya soma yi, na kasa hakura ne wlh nace sai na zo na duba ku, kawai zan tafi gobe zan dawo, sai mu yi hiran yaushe gamo." Bintu tace, "kai don Allah ki tsaya mana, ga abinci ma ina yi idan na sauke mu ci tare, amma daga zuwa kuma ki ce za ki tafi? Ko kin je har gidan su Yaya Naziru ne?" Before tayi magana sai ga sallaman Bashir ya shigo gidan yana kwaɗa kiran ta Tashi tayi da sauri ta fita, Bintu ma ta bi bayanta tana amsa sallaman "To leda mai yawon banza, ashe kina nan ne ana neman ki? Daga zuwa gari kin soma yawo, ashe kina nan da halin ki wato? To mu je gida Baba na kira." Hararansa tayi tace, "Ni fa ba na son takura, daga zuwa zaka zo ka fara damuna, yaushe na zo gidan ne?" Kunnenta ya murɗe yana faɗin, "ƴar banza, dama Ni kaɗai ne ban yi kewar ki ba don bakin nan naki na rashin kunya, kin dawo kenan, wlh ba ƙyale ki zan yi ba nima hali na yana nan tafka za ki sha, ina tunanin kafin ki koma inda kika fito sai na ƙara ma bakin nan tsini." Hannunsa ta buge sabida zafin da ta ji, lokaci guda ta tsuke fuska tana cewa, "Allah ya isa mugu azzalumi, wai kai meyasa halin mugunta ka iya kodayaushe?" "Ni kike kira mugu Meramu? Ai kuwa yanzu zan yi maganin ki." Hannu yasa ya tallabo mata ƙeya yana dariyan mugunta, Bintu na ba shi haƙuri amma bai ƙyale ta ba yana cewa, "babu ruwanki, ki bar Ni da yarinyar nan mara kunya, har yanzu ashe bata yi hankali ba?" Da gudu Maryamu ta ruga tabar gidan tana zagin shi, Ai kuwa ya runtuma aguje ya bi bayanta, Dayake akwai dogayen takalma a ƙafanta nan da nan ya kamo ta ya ci gaba da tallabe mata ƙeya yana tsokanarta, Ita kuma tana zagin sa tana kuka wi-wi, domin duk yanda ta so ta kufce mishi ta kasa Bashir da akwai mugunta, ba abun da yake so illa ya ga yana cin zalunta, ita kuma da bakin rashin kunya ta dinga zagin sa kenan kamar ba Yayanta ba, yace, "shegiya da bak'ar fuska, ashe har yanzu kina kukan babu hawaye?" A haka ya iza ƙeyarta suka shiga gidan Tun a sauro suka soma jin ihun ta "Ah ah; Kai Kai! Bashir kanka ɗaya kuwa? Kai da aka ce ka kira ta shine ka taso ta gaba kana tallabe ta kamar yanda ka saba ko? Ashe halin ka na  banza yana nan?" Jin muryan Babansu yana wannan maganar, shiyasa Maryamu ta ƙara volume ɗin kukan ta kamar gaske, wurin Baban ta nufa tana cewa, "wlh bazan yarda ba sai an bi min hakkina, wlh Baba tun a can gidan Bintu yake naushina a ciki yana murɗe min kunne kamar zai kashe Ni, cewa ma yayi ai haushina yake ji dama ya rabu da duka na." "Wlh Baba ƙarya..." "Yi min shiru mutumin banza, kai baka san yanzu ta wuce duka ba Bashir? Ba na son wannan shirmen na wasan banza, kar in ƙara ji." Umma Jummai tace, "ai tun farko ban so ya je kiran ta ba, tunda ya ji an ce ta zo a kira ta, yace shi zai je, na san dama da mugunta a ranka wlh, Bashir ba ka jin magana duk ka sa ta raina ka a banza a hofi." Baba kuwa hannun Maryamu ya ja yace, "ta zauna gefensa." Yana ci gaba da ma Bashir ɗin faɗa tare da cewan, "zai haɗa shi da su Ashiru in suka shigo tunda bai jin magana." Maryamu sai dad'i take ji tana masa dariya ƙasa-ƙasa. *** _____A takaice a Zaria Maryamu ta ƙarisa hutun ta gaba ɗaya, wata ɗaya tayi da satikai a can, ba ƙaramin dad'i ta ji ba don ba kaɗan ba tayi yawo kamar yanda take so, tunda a can basu da lokaci koyaushe suna karatu, shiyasa hutun nan da tayi a garin su ga ta ga ƴan uwanta, ba ƙaramin farin ciki tayi ba, daga ƙarshe ma daga gidan Iya Samira aka zo ɗaukar ta, Ammee ta aiko driver tun daga Abujan ya zo ya tafi da ita, Suma can sun yi murnan dawowanta since sun yi kewarta sosai A satin suka ci gaba da zuwa makaranta, S.S 2 kenan, har yanzu kuma suna koyon computer duk da kaɗan ya rage a yaye su. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____Sadiq shima a wannan time ɗin ya gama graduation ɗin sa, har an nema masa makaranta a can England kamar yanda su SHAREEF suka yi, zai tafi nan da kamar watanni uku masu zuwa zai wuce Fannin SHAREEF dai babu abun da ya sauya yana can yana fama da dakon soyayyar Haseena, wanda ya rasa dalilin sauya masa da ba ta buƙatar farin cikin sa a yanzu, ga shi yanzu irin son da yake mata ko kaɗan ba ya iya mata faɗa, ba ya son ma abun da zai ɓata mata rai, duk abun da tace eh ko yana so ko ba ya so; eh ne a wurin sa, idan tace a'a ma haka, yana cikin wani hali da buƙatar Mace da ke damunsa, ba ta tsinana masa komai koda ya je wurin ta, sai dai ya ƙara wa kansa matsala tunda bazai samu yanda yake so ba, duk yanda zai nuna mata halin da yake ciki ta gaza fahimtar shi, sau tari yana ganinta da Nana idan ya je can, amma duk faɗan da zai mata da son daƙile alaƙar su, Ta nuna masa, "sam babu ruwansa ya ƙyale su." To dayake ba ya son ɓacin ranta sai dai ya haƙura yana ganin su tare ba shi da yanda zai yi, domin ya fahimci cewa alaƙar su da Nana shiyasa Haseena ta soma gurɓacewa ta canza mishi, tunda a zahiri yana kallon wasu ɗabi'u irin nata da take yi, abun ya soma damunsa, ga ba kwanciyar hankali kullum yana faman neman magani a kan matsalar sa muddin in sha'awa ta tashi mishi, shiyasa damuwar da ya sanya wa ransa a haka ya soma ramewa yana fita a hayyacin sa, duk ya sauya kamar ba shi ba Iyayensa tun abun ba ya damunsu, har sun soma bincikar shi ko zai faɗa musu gaskiyar ainihin abun da ya sauya shi lokaci guda, domin ko magana wannan SHAREEF bai cika yi ba yanzu, dama can miskili ne a idon jama'a, to yanzu abun ya shafi har gida ba sa ganin walwalan sa, idan ya zauna ba abun da yake yi sai tunani, yawancin lokuta ma yana yawan rashin lafiya, su basu san ciwon mai yake yi ba amma idan sun bukaci su sani sai dai yace musu, "ciwon kai ne.". To tun yana ɓoye wa yanzu sun soma fahimtar yanayin ciwon nashi kamar yanda Likita ya taɓa musu bayani, tunda ciwon ciki bai cika ɓoyuwa ba, Abun yana damunsu matuƙa, amma kuma ai sun san har da taurin kai irin nasa, sun masa gata amma ya nuna ba ya son hakan, ita wacce yake ƙauna tana can wani wurin tana karatu baza ta amfane sa da komai ba, wacce suka ba shi ya nuna ba ya sonta, Sun zauna sun masa nasiha mai ratsa zuciya a kan ya taimaki rayuwarsa tun wuri ya amince da auren Maryamu ta dawo nan da zama, wataƙil zai samu lafiya tun kafin hakan ya fi ƙarfin sa, Amma har yanzu SHAREEF maganarsa ɗaya ce ya kafe ba ya son hakan, ya ƙi nuna musu amincewar sa, Abun yana basu mamaki, shiyasa suka ƙyale shi, idan ya ji jiki don kansa zai dawo kan hanya, zai nemi taimako a wurin su Inda gefe ɗaya ma Hanif yana ta nuna masa illan hakan, da ya zauna da cuta gwara ya nema wa kansa mafita, amma ya ƙi sauraren su A ganin shi zai iya da matsalar shi, idan ya sha magani yana samun sauƙi sosai, sai dai idan ya tashi masa dole sai ya zauna jinya Hanif ma ya fita harkansa don shima yana fama da tashi matsalar, saboda a yanzu Dady ya faɗa masa, "gwara shima ya nemo Matar yayi aure tunda lokaci ya soma ja." To dayake a yanzu Hanif shima yana buƙatar auren, musamman yanzu da ya tabbatar wa kansa yana matukar ƙaunar Amra, duk da har yanzu bai faɗa mata ba, amma gaskiya yana bata kulawa ainun, don yanzu ya saba da ita sosai da sosai, har gidan su yana zuwa, duk ranan da SHAREEF bazai je aiki ba, to idan zai fita da kansa yake zuwa gida ya ɗauke ta, kuma shi zai mayar da ita, A taƙaice dai har ƴan gidan su Amra sun san shi tunda suna shan labarin sa a wurin ta, Shigowar sa cikin rayuwarsu ba ƙaramin taimakon su yayi ba, tun suna ɗari-ɗari suna mamakin irin taimakon da yake musu, daga baya da suka fahimci halin sa sai suka saki jikin su Akwai wani ranan ma da ya zo ɗaukar Amra, a nan ne ya tarar da Jabir ya zo gidan yana ci musu mutunci, sai zagin su yake yi yana kumfar baki, Abun ya ɗaure mishi kai sabida yayi mamakin saurayin matuƙa, kuma tabbas ya gane sa tun ranan farko da ya taɓa ganin sa ya ga tsoro a idanun Amra, Yanzun ma ga shi ya ga ya janyo ta yana ƙoƙarin barin gidan da ita, Sun fito zaure yana kiciniyar barin gidan da ita da ƙarfi Tana kuka tana ƙanƙame jikinta, Yayinda su Afra suma sun ƙanƙamo ta sunan kukan suma Mama na faɗin, "ina zaka kaimin ƴa Jabir? Wai baka da tausayi ne baza ka sakar min ɗiya ba?" Karaf sai ganin Hanif suka yi ya shigo cikin zauren hankali a tashe yana cewa, "lafiya Mama? Me ke faruwa ne?" "Yauwa Hanif, don Allah ka taimaka mana, wannan banzan Yaron ne ya zo zai tafi min da yarinya, ya je yayi shaye-shayen shi ya zo yana mana hauka a nan, ba irin yanda ban yi ba don in kuɓutar da ita amma mun gagara, dole sai ya tafi da ita." Kallon Amra yayi wacce take ta faman kuka ita da ƴan uwanta, tana riƙe gam a hannun Jabir wanda ke layi idanunsa suna ƙin buɗe wa sabida shawuwan da yayi, Sai sambatu yake yi yana ci gaba da zage-zagen sai ya tafi da ita, Hanif cikin rashin fahimta yake ƙara kallon Mama da cewa, "to Mama, shi ɗin waye ne da zai tafi da ita? A kan me?" Cikin kuka Afra tayi tsulum tace, "wlh Yaya babu abun da ya haɗa mu dashi, kullum sai ya zo ya ci zarafin Aunty Amra sabida mugu ne azzalumi, har dukan ta yake yi, ba abun da ya haɗa mu dashi wlh." Hankalin Hanif yayi ƙololuwar tashi da jin abun da Afra take cewa, musamman da ya ji ta ambaci duka, shiyasa ya saka hannu lokaci guda ya finciko rigan Jabir; sai ga shi ya wantsalo gabansa, Hannu ya sanya ya sharara mishi mari sabida yanda lokaci ɗaya ransa yayi ƙololuwar ɓaci, "Kai dan Ubanka shaye-shayen naka ne yake faɗa maka ƙarya da zaka zo gidan mutane kana iskanci? Waye ya baka permission ɗin shigowa gidan mutane?" Idanunsa jawur Jabir yake kallon Hanif sabida ba ƙaramin shigan sa marin yayi ba, shiyasa cikin hargowa cike da fitan hayyaci irin wanda ya sha yayi tatul; kansa ba noti yake cewa, "Ni ka mara dan du**rn uwarka? Kai uban wa ya kawo ka gidan nan da zaka shiga tsakanina da Matata? Wlh na rantse da Allah sai na kassaraka tunda kayi ƙoƙarin raba tsakanin mu, babu wani shege da ya isa ya hana Ni abun da nayi ninya." Sai ya kama ihu yana ɗaga hannu da faɗin, "kai ba a haife ka ba wlh, yau sai na nuna maka waye Jabiru a garin nan, baka sanni ba ko?" Ya zazzaro mishi ido yana cije baki irin na tauraye Sakin sa Hanif yayi tare da ƙoƙarin nannaɗe hannun rigansa yace, "ban sanka ba sai ka faɗa min wane ne kai, Ni kafin ka ɗauki mataki a kaina zan dawo da kai cikin hayyacinka yanzu." Da sauri Mama ta hana shi taɓa shi sabida ganin abun da yake shirin yi, Tace, "don Allah kar ka biye wa wannan Yaron bai da hankali bai san abun da yake yi ba, ka ƙyale sa kawai tunda Allah ya kawo ka ka ƙwaci Amra, wlh bai da mutunci komai zai iya yi, Mahaifinsa shi yake ɗaure masa gindin duk abun da yake yi, bamu san mai muka tare musu ba amma koyaushe cikin cin zarafin mu suke yi, musamman ma ƴata da ya hana ta saƙat kullum cikin fargaba da tashin hankali take sabida tunanin abun da zai mata." Sai ta dubi Jabir ɗin da ke kumfar baki yana zazzare ido like a ɗan daba, tace masa, "ka fitan mana a gida matsiyaci kawai, kuma wlh kotu zata raba mu da kai duk ranan da ka zo gidan nan ka sake taɓa ta, banza shashasha mara tunani." "Au haka kika ce ko? Wlh summa tallahi sai na jijjiga muku bala'in da baku taɓa gani ba a arean nan, kuma wannan yarinyar bata da Miji sai Ni sai ta zama tawa ko ta halin ya-ya ne, ko ku aura min ita da arziki ko na danne shegiya a lungu sabida..." Wani irin naushi Hanif ya tattakura yakai mishi a mouth din sa, cikin wani irin fushi ya shaƙo wuyansa kamar zai kashe shi yace, "kai ƙaramin ɗan iska buɗe idanunka ka kalle Ni da kyau, duk ranan da kayi gigin sake taɓa yarinyar nan; wlh sai na kashe ka, sai na illata maka rayuwa, sai na ɓatar da kai dan Ubanka, jujin da ke kanka zan sauke maka, ɗan iska kawai fita." Ya tura sa zuwa waje ya bugu da bango Sosai Jabir ya ji jiki da irin shaƙan da Hanif yayi masa, musamman turo sa da yayi waje ya buga kansa, hakan ya fusata shi shima yana kallonsa ya soma antayo masa zagi ta uwa ta uba, irin na gogaggun ƴan duniyar nan, yace, "billahil lazi ka jira Ni nan da mintoci zaku ga mai zan muku gaba ɗayan ku, bari in dawo." Ya miƙe kamar wanda zai kifa ya bi hanya yana haki tare da ɗaga murya yana cewa, "ku jira Ni yanzu zan dawo dukkan ku sai na karku." Su Mama hankalin su ya tashi matuƙa, domin sun san bazai wuce ƴan daba Abokansa zai kira ma Hanif ba, Shi yasa Mama tace mishi, "ya tafi kawai, domin ta san ƴan iskan Abokansa zai kira su yi mishi wani abu, kar wani abun ya same shi a ga laifin su gwara ya tafi." Hanif yace, "a'a Mama, babu inda zan je, in har a kan wannan Yaron ne babu inda zan je, ina zuwa." Sai yayi saurin laluba aljihun sa yana neman wayansa, Tunawa da yayi yabar ta a Mota shiyasa ya fice da sauri ya koma wurin motan nasa har da ƙara wa da gudu, saboda Motan da ɗan tazara daga wurin gidan su, Zuwa yayi ya dauki wayan ya lallatsa ya kira Police, Sai da ya kira su ya tabbatar suna kan zuwa before ya wuce gidan, already sun shiga cikin gidan shiyasa shima ya shiga ciki, A zaune ya gansu a bakin ƙofa har yanzu Amra tana kuka, While su Afra suna matsan hawaye duk hankalin su yayi matuƙar tashi Ita kanta Mama ƙarfin hali take yi amma ta san cewa yau ɓarnan da Jabir zai jawo musu ba kaɗan bane, Shi yasa tana ganin Hanif ya dawo tace, "don Allah Hanif ka tafi kar wani abu ya same ka mu shiga uku, wlh Yaron nan bai da hankali na tabbata tunda ya furta hakan Abokansa yan iska zai kira, bamu san da me zasu zo ba." "Kar ki damu Mama, nima na kira ƴan sanda kuma yanzun nan zasu ƙariso, ko ma mene ne zan ɗauki mataki a kansu hakan baza ta sake faruwa ba." Yayi furucin yana ƙara kallon Amra da ke kwance a jikin Mama tana sharɓan kuka, Idanun nan sun kaɗa sun yi jazir duk ta fita a hayyacinta, Wani irin zafi yake ji a ransa sabida ganinta a irin wannan halin, Tabbas yau zai koya ma Yaron nan hankali, bazai ƙara gigin taɓa mishi Amra ba, domin in har a kanta ne zai iya daukar mummunar mataki a kan duk wani wanda zai ci zarafin ta, Hanif bai iya fushi ba amma in yayi ba ya kyau; don yana da zafin rai shima sosai, duk da yana da saurin sauka A lokacin da su Jabir suka dawo, yayi dai-dai da zuwan ƴan sanda, domin har sun soma dukan Motan Hanif zasu farfasa ta, Sai ga su sun taho a sukwane, Dayake Hanif ya fito sabida jin shiru basu iso ba ƴan sandan, shiyasa ya fita sabida hankalin sa ya kasa kwanciya kar su Jabir su zo su rutsa shi a cikin gidan, gwara ya fita ya duba ta inda zasu taho, Yana hango lokacin da suka taho suka soma dukan Motan nasa, Abun ya ɓata masa rai, bai yi la'akari da yanda suka taho a gigice da makaman yaƙi ba, kowannen su riƙe da adda a hannu, a zafafe ya nufe su da ninyar afka musu shima; don ransa yayi matukar ɓaci yanda suke son illata masa Mota, Sai ga diran ƴan sanda a wurin, Nan take ya basu umarnin su kama su, Duk da sun so guduwa amma haka aka cafke su dukka aka saka su a Mota, Kafin wani lokaci wurin ya cika da jama'a suna kallon abun da ke faruwa, duk da basu san me ke wakana ba, amma a kan idanunsu aka wuce da su Jabir, Nan fa suka tabbatar da cewan sun taɓo abun da ya fi ƙarfin su tunda har aka kawo ƴan sanda suka kama su, Dayake sun san su fitinannu ne, ko ƴan sandan shakkar kama su suke yi, sun bi sun addabi Jama'ar anguwar, sai ga shi yau sun haɗu da dai-dai su tunda har aka iya wuce wa dasu. [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱          *SHAREEF*               _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE8* _____Hankalin su Mama har ya kwanta da suka ga ƴan sanda sun wuce da su Jabir, Kuma Hanif ya sake kwantar musu da hankali sosai yace, "za a ɗauki mataki a kansu, daga yanzu babu abun da zai sake faruwa." Mama sai godiya take masa har da hawayenta, sabida farin cikin yanda ya damu da su sun samu wanda ya damu da lamarin su Amra bata so zuwa aikin ba, amma shi ya matsa mata yace, "ta shirya su tafi." Hijab kawai ta saka tunda already tayi wankan ta, dama suna cikin karyawa ne Jabir ya zo musu da hatsaniya, Kuma duk yanda Mama ta so ta ci wani abu before su tafi amma ta ƙi, domin bata jin daɗin jikinta sabida yanda duk ta firgice Jabir ya ɗaga mata hankali, ga kukan da ta sha, don Hanif ne ya matsa mata ma da baza ta fita ba a yau, amma bata da yanda zata yi tunda tana ganin girman sa baza ta iya masa musu ba, dole ta saka hijab ta dauki jakarta suka tafi Su kuma su Afra ƙarshe sai dai suka zauna a gida tunda time ya ƙure musu a gida, ko sun je makarantar yanzu ba lallai a bar su su shiga ba. *** _____Tunda suka shiga Motan suka fara tafiya, Amra ta takure jikinta ta kafa wa hanya idanu ko motsi ƙwaƙƙwara ta kasa Yayinda Hanif ke tuƙin a hankali shima idanunsa a kan titin, ganin shirun yayi yawa shiyasa ya dube ta yana ɗan jan numfashi, idanunsa ba abun da suke tuna masa sai surar jikinta wanda ya gama gani a gidan su, bai taɓa tunanin haka take da kyau ba sai a yau; since bai taɓa ganinta da gyale ko da ƙaramin Hijab ba, koyaushe da dogon hijabi take zuwa, face ɗin ta kaɗai zaka iya gani sai idan ta fito da hannayenta, Shi kansa yana son yayi mata wata tambaya da ya tsaya mishi a rai sabida yanda take yawan saka baƙin Hijab, a kullum dashi take zuwa, dole yana son ya san aƙidan ta gudun samun matsala; tunda har a zuciyarsa ya amince ta zame mishi Abokiyar rayuwa, Ganin yanda ta takure ta ƙi sakin jikinta har yanzu, shiyasa ya kalle ta ya kira sunan ta Kallonsa tayi; da idanuwanta da suka rine suka yi ja duk sun kumbura, face ɗin ta babu fara'a, Janye idanuwanta tayi sabida jin hawaye suna son zubo mata Hanif kuwa ji yake yi tamkar ya rungumo ta a jikinsa ya rarrashe ta sabida yanda yake jin tsananin kaunarta da tausayin ta a rai, ya san tana cikin damuwa sosai kuma yana neman hanyar da zai faranta mata, shiyasa a natse cikin kwantar da murya yake cewa, "Please Amra ba na jin daɗin ganin ki a wannan yanayin, sam zuciyata ba ta min dad'i musamman idan na kalli wannan kyakkyawar fuskar taki na ganta cikin damuwa." Da sauri ta kalle sa sabida jin abun da yace Sai ya sakar mata tattausan murmushi yana cewa, "Zan fi jin dad'i idan muna tare na riƙa ganin wannan murmushin naki mai ƙara miki kyau da haiba, ki manta da wannan Yaron babu wanda ya isa ya sake ɗaga hannu ya taɓa ki in har ina tare da ke, nayi miki wannan alkwarin, amma sai dai..." Sai yayi shiru yana cije laɓɓa, yayinda yake kallonta cike da so da ƙauna Ita kuma ta kasa ɗago kai ta sake kallonsa duk da kalaman nasa suna mata dad'i, wanda nan take suka soma sanyaya mata zuciya tare da yaye mata damuwarta, Shiru tayi tana sake kasa kunne da jin zantukan shi A cikin cool voice mai ratsa zuciya still ya kira sunan ta Wanda hakan ba ƙaramin faɗar mata da gaba yayi ba, ɗakyar ta ɗago kai tayi mishi duba ɗaya tayi saurin janye idanun sabida kallon da yake mata, wanda take kumburarrun idanuwanta suka nitse cikin nasa, baza ta iya juran kallonsa bane sabida yanayin kallon da yake sauke mata, dalilin da yasa ta duƙar da kanta kenan tana murmusawa a hankali Karon farko da ya ga face ɗin ta da murmushi shiyasa shima ya sake sakin murmushin yana jin a ransa zai yi nasara Insha Allahu, "ina son in tambaye ki a kan wani abu, but kar ki yi min wata fahimta daban sabida akwai maganar da zamu yi daga baya. Zan iya sanin aƙidan ki?" Shiru tayi tana maimaita tambayan a ranta duk da bata fahimci mai yake nufi ba Shi kuma ganin tayi shiru kuma ta ƙi kallonsa, sai ya sake cewa, "i know za ki ji tambayar tawa wata iri, but kawai don na ga kina yawan saka baƙin Hijab ne shiyasa nake tambayar ki, sabida na ga ƴan Shi'a suka fi saka wa." Ɗago kai tayi ta kalle sa, sai tayi murmushi mai sauti wadda fuskarta tuni ta washe alamun maganar nasa ne ya bata nishaɗi, Hannunta ta ɗaga tana masa bayani bakin ta a washe Dariya yayi yace, "kin san ba na gane Yaren nan naki, amma very soon zan koya ko don sabida ke, sabida ke; ke kaɗai." Ya ƙare maganar cikin wani salo yana zuba mata ido kamar zai cinye ta Da sauri ta ɗauke nata idanun cikin jin kunyarsa, sai dai ta kasa wani motsi sai murza hannayenta da take yi idanunta a kan titi "Oya, faɗa min mana, ki rubuta min text ina son sanin amsar ki." Wayanta ta ɗauka cikin jaka, ta soma mishi typing, after ta gama bata tura ba sai ta miƙa masa wayan ya amsa "Ni ba ƴar Shi'a bace, It's just that it's my favorite color, I really love the black color very much, that's why kodayaushe nake sanya baƙin Hijab." Yayi mamakin amsar nata, kuma ta burge sa, shiyasa ya dube ta yace, "but any time kalan kike saka wa, why don't you change?" Shiru kawai tayi tana ci gaba da mirza yatsunta While shi kuma sai ya ajiye mata wayan nata yana faɗin, "yau ina son in faɗa miki wata magana mai muhimmanci, but sai dai zuwa anjima idan mun fito daga meeting zan neme ki." Kanta ta ɗaga masa har yanzu bata kalle sa ba, idanunta na a kan cikin companin da suka shigo Shima bai yi magana ba har ya dakatar da motan, Sannan ya leƙa back sit ya dauko Jakarsa Itama wayanta ta ɗauka tunda tana jin sanda ya ajiye, Kallonsa tayi but ganin yana shirin juyo wa gare ta, sai tayi saurin ɗauke idanunta a kansa ta buɗe motan da sauri ta fice Murmushi kawai yayi yana dubanta, har cikin zuciyarsa yake jin farin ciki a tare ita, yau dai dole zai bayyana mata irin tarin ƙaunar da yake mata, ya shirya tsab domin fuskantar ƙalubalen sa, Da zaran ta amince dashi zai gabatar da ita a wurin Iyayensa; domin sanin wace ce ita, Kuma yana da yaƙinin Insha Allahu zasu fahimce sa, shi yake da burin zama da ita a haka, kuma Insha Allahu bazai taɓa samun matsala ba daga wurin Iyayensa Har ya fito tana tsaye tana jiran sa domin ta kasa tafiya, Sai da ya fito sannan ta zagaya side din sa tana mishi nuni da ya bata Jakar sa ta riƙe Fahimtar hakan shiyasa ya girgiza mata kai yana ƴar dariya kaɗan, tare da furta, "no ki bari kawai, ba na fatan in sanya Gimbiyyata irin wannan aikin mai wahala. Mu je kawai." Ya nuna mata hanya yana zuba mata murmushin sa mai kyau Zuciyar Amra gaba ɗaya ta soma mata wani iri sabida yanda take jin gabanta yana faɗuwa a game da kallon da Hanif yake mata da kuma kalaman sa, amma sai ta daure ta janye idanuwanta before tayi gaba yana bin ta a baya, gaba ɗaya tana jin ta a takure musamman yanda ya tasa ta a gaba, tana ji a jikinta ita yake kallo shiyasa ta sake natsuwa sosai tana tafiyarta a hankali gudun kar ta harɗe; cus yanda take ji a jikinta da jin idanuwansa a kanta Bayan sun isa office ɗin, sun tarar da Secretary ɗin sa har ya zo ma, Yana ganin Hanif ɗin yayi saurin amsar mishi Jakansa yana masa welcoming Itama Amra sai tayi masa sannu ta wurin ɗaga masa hannu tana washe masa baki Murmushi yayi ya ɗaga mata hannu before ya bi bayan Hanif da sauri suka shiga office ɗin Amra zama tayi a kan kujerar ta tana sauke numfashi a hankali, shiru tayi tana tuna fuskar Hanif, a ranta tana mamakin kirkin sa, babban Mutum dashi amma ya kasance mai taimaka mata, bai ɗauki kansa a bakin komai ba yana hurɗan shi babu girman kai ko wani isa na masu shi, Gaskiya shi alheri ne a rayuwarta, tabbas ya taimaka mata sosai a rayuwa, tana son tayi mishi godiya a kan abun da yayi mata yau, Amma ta yanke shawarar zuwa anjima in zasu yi maganar da yace, zata nuna masa godiyar ta, Tana nan zaune har Secretary ya fito ya taho wurin ta yana mata dariya, Cikin faram-faram suka gaisa duk da shima ba wai ya iya Yaren su bane, amma suna yawan chart a waya since yawanci shine mai kula da ita, kuma mataimakiyar sa ce tare suke aiki Yanzun ma aikin suka ɗaura suna yi suna ɗan taɓa hira, duk da shine yake bata bayanan a kan aikin nasu, ko ya sako wasa a ciki, Ita dai sai dai tayi murmushi ko dariya, in da yiwuwar ta maida masa da martani sai tayi masa typing a kan waya ya karanta Ƙarfe biyu suke da meeting, Zuwa ƙarfe daya suka tashi a aiki, Daga nan masallaci suka wuce kowanne ya gabatar da Sallah before suka yi lunch, After an dawo daga break sai suka wuce meeting Yau SHAREEF bai zo ba dole Hanif ne yake jagorantar komai tunda hakan suke yi, Masu offices- offices da su aka yi meeting ɗin, Sauran ma'aikatan kuma suna bakin aiki Amra ita kaɗai ce a office tana faman aiki, since Secretary tare da Hanif suna can tare a wurin meeting ɗin, Bata san da shigowar ta ba sabida hankalin ta na a kan computer tana faman daddanna wa, Sai sallamanta ta ji a dab da ita, Da sauri ta ɗago kai tana kallon Matashiyar budurwan da ke dab da ita, wanda a haife baza ta fi 19years ba Tana sanye cikin riga da wando wanda ta ɗaura Red colour na Abaya, sai tayi rolling da mayafin shi, face ɗin ta babu MakeUp amma ta saka red colour na janbaki ya ji raɗau, Ƙafafunta sanye cikin Black cover shoes masu ɗaukar hankali, Ta rataye hangbag ɗin ta tana riƙe da wayanta a hannu Ido Amra ta zuba mata tana kallonta Hakan ne yasa Haajara ta yatsina face tana faɗin, "kina jin ina sallama, ko ba kya amsa wa ne?" Kanta ta girgiza mata tana sakin murmushi tare da ɗaga mata hannu Haajara tace, "tofa, alamu da Kurma nake magana kenan?" Kai ta ɗaga mata still face ɗin ta da ɗan yalwan fara'a Ita kuma sai ta ja tsaki tana nufan office din Hanif ba tare da ta sake magana ba, Koda ta shiga ta ga babu kowa sai ta dawo tana kallon Amran tare da cewa, "wai ke da gaske Kurma ce kenan? To ya aka yi aka ɗauke ki aiki tunda ba ki da wani amfani a nan? Taya ya za ki yi min bayanin inda ya tafi?" Shiru Amra tayi sabida sam kalaman Haajaran basu yi mata dad'i ba, shiyasa ta kasa mata bayanin komai sai kallonta da take yi While Haajara ta bi ta da kallon ƙasƙanci tana jan guntun tsaki, tare da ja da baya ta nemi wuri ta zauna tana harɗe ƙafafu, ta soma latsa wayanta batare da ta sake kallon inda Amra take ba Itama dai bata sake bi ta kanta ba tunda ta ga ta zauna, sai ma ci gaba da aikin gabanta da tayi har sanda su Hanif suka dawo Yayi mamakin ganin Haajara a office din nasa, cike da mamaki fuskarsa da ɗan fara'a yake cewa, "Haajara, ke ce?" Tashi tayi tana masa murmushi da faɗin, "wlh kuwa, na zo nan kusa da ku ne shine nace bari in zo mu gaisa, and kuma na je office ɗin Yaya SHAREEF aka ce min bai zo ba shine na zo nan." "Ok mu shiga ciki." Yayi maganar yana yin gaba zuwa office ɗin sa Bayansa ta bi suka shiga ciki, after sun zauna ta gaishe shi fuskarta da murmushi har yanzu Ya amsa ta yana faɗin, "ya mutanen gidan? Kowa lafiya ko?" "Alhamdulillah, ya aikin naku?" Kafaɗa ya ɗage yana ware hannunsa da ɗan dariyansa yace, "aiki da dad'i zamu ce, amma ba dad'i." Dariya tayi tace, "kai Yaya Hanif, da daɗin dai tunda ga shi nan har ya sauya ka har wani ƙiba kayi, mun daɗe bamu haɗu ba sai yau, Kodayake dama Yaya SHAREEF ne yake zuwa but kamar baka sanmu ba; har yanzu baka sake takowa inda muke ba." "To ban da abunki, mai zan zo in yi? Since itama Matar Bro ɗin ba ta nan kinga babu abun da zai kawo Ni." Ɗan gyara zamanta tayi cikin yanga cike da kwarkwasa tace, "ai ba sai wajen Aunty Haseena zaka zo ba, ko wurina ai yakamata ka riƙa zuwa muna gaisa wa tunda dai yanzu an zama ɗaya." Ɗan waro ido yayi waje, sai dai bai ce komai ba yayi murmushi yana ɗauke kai a kanta Ita kuma sai ta canza maganar da faɗin, "amma zuwa jibi ai Aunty Haseena zata dawo, zaka iya ganin mu a gidan ku at any time, but Ni dai zuwan domin ka zan yi tunda kai baza ka iya zuwa domina ba." Dubanta yayi, sai dai yanayin yanda take mishi wani kallo tana murmusawa, sai ya ɗauke kai yana ɗan taɓe baki da cewan, "Haajara, ai ni ba abun da zai sake kawo Ni gidan ku sai dai in Brother, shine yake da damar zuwa ba Ni ba." "Haba kai kuwa, kana Ƙaninsa kuma ka ce babu abin da zai kawo ka? Gaskiya ban ji daɗin maganar ka ba don gani nake yi kamar baka damu da mu ba, but Ni gani na zo duba ku sabida na san ku nawa ne. Gaskiya ba na son alaƙar mu ta tsaya a haka Yaya Hanif, zan so mu ƙulla Abota ko ba don Aunty Haseena ba." "Ayya, Ni kuma ba na Abota da Mace, zan dai iya ɗaukar ki a matsayin Ƙanwata, hakan yayi miki?" Murmushi tayi duk da bata ji dad'i ba, sai ta margaya kanta da faɗin, "eh yayi, na ji dad'i a hakan ma." Shiru ya ɗan ratsa saboda ya ci gaba da aikin sa bai sake mata magana ba, Jin tayi shiru kamar ruwa ya ci ta sai ya ɗago yana kallon ta, da mamakin sa gani yayi ta zuba mishi ido kamar zata cinye sa, Amma sai kawai ya basar yana cewa, "ba yanzu za ki tafi bane?" Maƙe kafaɗa tayi tace, "No ba yanzu ba, ina son in ɗan ƙara lokaci a nan muna hira, hakan zai fi faranta min rai." Shiru yayi mata duk da yana son fahimtar mai take nufi a yanda take masa kwarkwasan nan, ba tun yau ba tun a ranan auren su SHAREEF ya soma fahimtar take-taken ta wajen shige masa "Yaya Hanif, idan baza ka damu ba zan so in samu numban ka sabida mu riƙa gaisa wa." Kamar bazai bata ba, sai ya ga hakan kuma bai dace ba, shiyasa yace mata, "to mai zai hana? Bari in karanto miki." Cikin jin dad'i ta soma latsa wayan nata tana rubuta numban nasa, ta ji dad'i yanda bai ce mata a'a ba, sai da ta gama tayi save before ta kalle shi tace, "please Yaya Hanif a ɗan kawo min wani abu na sha mana, sabida ƙishi nake ji." "I'm sorry na manta ne wlh, ga fridge can za ki iya daukar duk abin da kike so, inyaso sai ki koma waɗancan kujerun zai fi miki daɗin zama." Haajara tace, "a'a nan ma ya isa, Ni da zan taya ka hira." Murmushi kawai yayi mata yana ɗaukar wayansa tare da latso numban Amra, ya shiga ya rubuta saƙon yana neman ta yanzu Ita kuma Haajara bata kai ga tashi ba wayanta ta soma ring, hakan ne yasa ta dakata tana ɗaukar wayan. *** _____Just like seconds sai ga ta ta buɗo ƙofan ta shigo; hannun ta ɗaya sanye a saman wuyanta tana gyara wa Hijabin ta zama, Idanunta ƙyam a kansa, ganin kallon da Hanif yake mata yana faman doka mata murmushi, shiyasa itama ta sakar masa tattausan murmushin ta tana ƙarisa wa wurin da suke Kallon da Hanif yake yi wa Amra ne ya jawo hankalin Haajara gare sa, dama ta gama wayan shiyasa ta katse tana bin sa da kallo tare da mayar da idanunta a kan Amran, Ganin yanda suka zuba wa juna ido sai da wani abu ya ɗarsu a zuciyarta, musamman yanda ta ga yana zuba mata murmushi da irin wannan kallon da sam hankali da tunanin ta ya gaza ɗauka, take ta soma jin wani iri tare da jin haushin Amran kamar ta make ta, Baki ta buɗe da ninyar yin magana, but sai Hanif ya riga ta yana yi wa Amran magana Tambayarta yake yi, "ta gama aikin da ya bata?" Tayi saurin ɗaga masa kai fuskarta a washe Sai ya ciro wasu files guda biyu yana mata alamun ta matso kusa dashi Babu musu ta zagaya ta side din sa tana matso wa dab dashi, Yayinda ta dubi files ɗin da yake nuna mata don ganin bayanin da yake mata Ita kuma hakan ya ƙara sanya Haajara cikin baƙin ciki, zuciyarta nan da nan ta soma hassala sabida kishin ganin su a haka gab da juna, idanu ta zuba musu sam ba ta jin abun da suke furta wa illa baƙin cikin da ya tokare mata wuya, ji take yi kamar ta je ta shaƙo wuyan Amra tayi jifa da ita sabida ganin yanda ta sake kusanci da Hanif ɗin sosai da yake mata bayani tana duban files ɗin gabansa, wanda hakan kamar zasu haɗe don har nimfashin junan su suke ji Dalilin da yasa Hanif ya shiga wani yanayi kenan, tare da muskuta zaman shi yana mata kallon soyayya, face ɗin sa ɗauke da murmushi yake duban ta da faɗin, "kin gane ko? Za ki iya?" Murmushi tayi masa, sai dai bata yi ƙoƙarin amsa masa tambayar nasa ba sai da ta ɗan ja da baya sabida ganin kamar fuskokinsu zai haɗe don kusancin su, wanda fuskantar ta da yayi ne yasa ta ji wani iri zuciyarta ta hautsine, lokaci guda ta kasa jure wa ta ɗan ja da baya tana gyaɗa masa kanta Smile yayi shi kuma yana sake faɗin, "in dai baza ki iya ba sai in ba Secretaryna yayi min." Hannu ta ɗaga mishi tana masa bayanin zata iya Ya fahimce ta shiyasa ya rufe files ɗin ya miƙa mata yace, "ok, ki je ki fara, idan kin gama sai ki kawo min zamu yi maganar da nace." Kai ta gyaɗa masa tana juyawa zata bar wurin Haajara da tsananin kishi ya cika ta har idanunta sun soma yin ja sabida jin ƙwalla na taruwan mata, ko ba a faɗa mata ba ta ga soyayya a idanun Hanif, tabbas akwai wani abu a tsakanin mutanen nan biyu, wanda a zahiri abun yake dole wanda ya gansu a haka ya fahimci akwai ƙauna mai ƙarfi a tsakaninsu, Da idanu ta bi amra da ke ƙoƙarin fice wa a cikin office ɗin, bata san sanda ta daka mata tsawa da faɗin, "kee zo nan." Da mamaki Hanif ya bi Haajaran yana kallo sabida jin abun da tace Yayinda itama amran da sauri ta juya tana kallon Haajara wacce ta tsare ta da idanunta da suka soma sauya launi, Ta nuna kanta da yatsa alamun ita take kira? "Ke nake kira, ko kinga wata a nan ne?" Tayi maganar a gadarance tana tsatstsare ta da ido Hanif yace, "lafiya dai Haajara? Me zata yi miki kike mata wannan kiran?" Dubansa tayi tana yatsina fuska, sai kuma ta tura baki cike da son burge sa, a shagwaɓe tace, "Kai Yaya Hanif, ruwa fa zata dauko min, na ga ai ƴar aikin ka ne that's why zan buƙaci ta dauko min ruwan a fridge." Mamaki ne sosai ya bayyana a kan face ɗin Hanif, Ba shi kaɗai ba har amra da tayi tsimi tana kallon Haajaran ta kasa motsa wa Ita kuma Haajaran ko a jikinta; ta sake kallon Amra tana wulla mata harara da kallon ƙasƙanci tace, "ki dauko min drinks a fridge Malama." "No, stop Amrah." Yayi saurin furta wa sabida ganin zata nufi wurin fridge ɗin, Sai ya kalli Haajara fuskarsa a tsuke yace, "wannan ba ƴar aiki na bane, itama aiki take yi a Companin nan, za ki iya zuwa da kanki ki ɗauko abun da kike buƙata." "To meye laifi don nace ita ta dauko min? Ni fa baƙuwa ce fa, kuma koda ba ƴar aiki bace a ƙarƙashin ka take aiki, zaka iya sanya ta ta ɗauko min da kanka." Jin abun da tace ransa ya soma ɓaci duk da shi ba wai ya cika saurin fushi bane, amma ya kula don ƙasƙanci Haajara take son aikan Amra, musamman yanda take magana a gadarance ya soma fahimtar take-taken ta, Don ya baƙanta mata yace, "wannan ta wuce yadda kike zato, aiki take yi a karkashina amma tana da matsayi sosai a wuri na, ba bukatar ki aike ta don nima ba ki ga ina aiken ta ba." Sai ya dubi Amra da ke tsaye har yanzu, fuskarsa a ɗan sake yace, "za ki iya tafiya Amrah." Murmushi tayi masa; tare da juyawa ta fice a cikin office ɗin tana jin daɗin abun da yayi domin ta Wanda hakan ba ƙaramin fusata Haajara yayi ba, ranta ya sosu sai dai ta kasa ƙwaƙƙwaran motsi bare tayi magana, Yanzu ta tabbatar da cewan bata da wani matsayi a wurin Hanif, kuma tabbas wannan doguwar yarinyar duk yanda aka yi Hanif sonta yake yi, Kamar tayi kuka haka take ji, amma sai ta daure ta hana bayyanuwar hawayenta a waje, tare da ƙoƙarin kame kanta tana miƙe wa da faɗin, "to zan tafi, sai mun yi waya kenan?" Ɗago kai yayi ya dube ta, sai yayi kamar bai fahimci halin da take ciki ba, kuma bai saki fuskarsa ba yace, "ok." Yana ɗauke kansa ya mayar saman computern sa Abun yayi mata ciwo, amma bata da yadda zata yi, dole ta juya ta fice jiki a sanyaye, Tana fita suka haɗa ido da Amra da ke zaune wurin zamanta, Amma tuni ta ɗauke kai sabida kallon da Haajara ta sauke mata Secretary ma tuni ya ɗago yana duban ta, bai ce mata komai ba shima ya ɗauke kansa sabida aikin da ke gabansa Sai da ta ɗauki kamar seconni tana aika wa Amra mugun kallo, wadda bata san ma tana yi ba, ta ja ƙwafa ta fice a wurin zuciyarta na tafarfasa, Lallai dole ta dauki ɗammaran shiga jikin Hanif, domin har ga Allah baza ta taɓa sanya a lamarin nan ba, ƙaunarsa ta shige ta baza ta iya rabuwa dashi ba, tana ganin wannan ƙasƙantacciyar wacce talauchi ya gama fitar da ita a hayyaci, baza ta taɓa cin galaba a kanta ba, domin nesa ba kusa ba ta kerewa Amra, ta fita aji da komai, bata da wayewan da ita take dashi, ta san hanyar da zata bi domin mallakar Hanif ya zama nata, domin ta san ko shi sai dai ya faɗa ƙarya; amma bazai taɓa zaɓan Amra ya barta ba, Hakan ne yasa hankalin ta ya ɗan kwanta duk da akwai zallan ɓacin rai a tare da ita, tare da baƙin cikin ganin Amran a tare da Hanif bata da yanda zata yi ta raba su wurin aikin su ɗaya, Tabbas da a ce ta ƙarisa karatun ta babu abun da zai hana bata maye gurbin Amra a wurin aikin nan ba, amma su juri zuwa rafi... [31/03, 4:32 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE9* _____Mama na cikin ƙullin alalen da zasu yi, tana zuba wa a leda tana bama Salma na ƙullewa, Ita kuma Afra tana cikin kichen tana hura wuta, Suna hira sama-sama sai ganin Baba Jafaru suka yi cikin hargagi ya faɗo musu gida babu sallama sai tsiya da ya ci ransa, Dukkan su sai da suka tsorata sabida ganin shi a fujajan yana kwaɗa kiran Mama Ganinta da yayi a zaune shiyasa cikin masifan da ya taho dashi yake cewa, "wato ke Shafa ba ki da mutunci ba ki da ragowar sa ko? Ba ki san inda ke miki ciwo ba da har za ki sa a kama min ɗa a rufe min, tunda ke matsiyaciya ce mai rama khairan da sharri, to wlh tun wuri idan ba ki kwance ƙullalliyar da kika ƙulla ba; wlh summa tallahi sai ruwan sha ya gagare ki a garin nan, sai na ci miki mutunci na wulaƙanta ki, ita asararriyar yarinyar naki da kike gadara da ita, tambaɗaɗɗiyar kan titi; to zan dauke su gaba ɗaya a hannunki inga iskanci, dama ai mu ne dolen su ko? To daga yau zasu koma hannuna inga uban da ya isa ya ƙwace su, in ban da asara irin naki ke kin isa kikai Yaro na station ki sa a rufe sa? Wlh sai inda ƙarfina ya ƙare sai na wulaƙanta ki." Mama da tuni ta tashi kan ƙafafunta sabida ganin yanda yake hargagi kamar zai faɗo mata, ba ƙaramin ƙona mata rai kalaman sa suka yi ba, shiyasa nan da nan har hawaye sun soma ɗiga a kan fuskarta take cewa, "sabida kai baka son laifin ɗanka baka bari ka ji mai yake faruwa ba ka hau kai kana faɗa, ai ka san mai yake aikata wa tunda ba tun yau ba nake kawo maka ƙaran sa amma ka ƙi ka ɗauki mataki, sabida son zuciya irin naka ɗanka ya fi ƴaƴan wasu, wlh nima bazan yarda ba duk abun da zaka faɗa sai dai ka faɗa, a wannan karon bazan taɓa yarda ka ci min zarafi ba daga kai har ɗan naka, Yara dai nawa ne ko? Babu inda zasu je muna nan tare, kuma da kake zancen na rufe maka ɗa, ka je can ka nemi wanda ya rufe maka ɗanka don sun tono wanda ya fi ƙarfin su ne shiyasa suka samu sakamakon su, ba wurina ba." "Ƙarya kike yi mutumiyar banza, ai an faɗa min komai ke kika sa aka kama su aka rufe su sabida wannan shegiyar ƴar naki, na san komai shi kansa Yaron ai tare suke da ƴar naki, dole ke kika saka ya rufe shi, to wlh zan iya Shari'a da koma waye in har a kan ɗana ne, kinji na rantse bazan bar ki ba a wannan karon ba tunda kika nemi cin min mutunci, ki saka ido ki ga matakin da zan ɗauka, gidan nan sai ya gagare ki wlh kuwa, dole za ki bar mana gidan ɗan uwa ki zuba Yaran ki tafi, idan kuma kin ƙi daga nan har kotu sai mun je, kina wasa da Ni ne." Ya buga mata yatsu cikin zafin rai da tafarfasan zuci ya juya zai fice Ita kuma Mama faɗi take, "wlh Allah ya fi ƙarfin ka ko me zaka yi sai dai kayi, a kan gaskiyata nake bazan taɓa bari ku zalunce mu ba, sai inda ƙarfina ya ƙare mugaye azzalumai kawai." Sai ta fashe da kuka tana koma wa ta zauna zuciyarta na zafi da tsananin ƙunci, Ta kasa ci gaba da ƙullin ma sai hawaye da take yi Tuni Salma da Afra sun zo wurin ta sun kewaye ta suma suna hawayen sabida baƙin cikin kalaman Baba Jafaru, basu san mai zai faru ba, amma tunda suka gansa a wannan mugun ɓacin ran sun san dole bazai musu da sauki ba, dama kaf ƴan uwan Babansu shine Mutum mara imani da zafin zuciya, yana da son kansa, bare yanda ya ɗauki alwashi sun tabbatar komai zai iya yi Mama kuma a shirye take ta ɗauki duk cin kashin su, dama bata da wanda zai tsaya mata ne, muddin suka ce zasu shiga tsakanin ta da ƴaƴanta wlh hukuma zai raba su, wannan karon baza ta taɓa yarda ba, koda Hanif bai taimaka musu ba sai inda ƙarfin ta ya ƙare, tana jiran sauran ƴan uwan nasa don ta san suma zasu zo su sauke mata kwandon bala'in, wlh baza ta yarda ba, a kan me zasu rika cin zarafin ƴarta? Mai ta tare musu? Yarinyar da take fama da kanta kuma baza su barta ta ji da abun da ke damun ta ba; sai sun ɗaura mata masifan su, mugaye azzalumai. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____Bayan Amra ta gama aikin nata, sai ta ɗauki files ɗin ta wuce cikin office ɗin Hanif Yana zaune yana waya da Mahmud a kan evidence ɗin da ya samu ya tura masa a WhatsApp, dalilin da ya kira kenan yana faɗa masa, "ya hau kan WhatsApp ya tura masa." Tunda dama Mahmud ɗin yanzu suna can Abuja jiya suka tafi tare da PA'n SHAREEF da wasu ma'aikata biyu, Yana kallon Amra har ta zo ta zauna idanunsa a kanta yana ci gaba da wayan Ita kuma ganin kallon da yake mata sai ta ajiye files ɗin tana duƙar da kanta ta soma wasa da hannun Hijabin ta, Sai da ya gama ta ji ya ambaci sunanta, hakan ne yasa ta ɗago da kanta tana kallonsa Murmushi yayi mata yace, "kin gama ne?" Kai ta ɗaga mishi itama tana maida masa da martanin Murmushin Agogon hannunsa ya duba sabida ganin lokaci, sannan sai ya dube ta yace, "maganar da nake so nayi da ke magana ce mai tsawo, I wish we had more time, but now it's prayer time, ina ganin idan mun je mun dawo sai muyi maganar; ko?" Ya ƙare maganar da ɗan ware mata ido yana ƴar dariya Hakan ne ya bata kunya sai tayi saurin janye ƙwayar idanuwanta a kansa tana murmusawa, tare da jinjina mishi kanta Sallaman ta yayi yace, "ta je in ya dawo sai ta shigo." Sai da ya ga ta fita before ya miƙe ya shiga toilet ya ɗaura alwala ya fita Time ɗin shima Secretary yayi alwalan har ya wuce, Itama Amra ta wuce side ɗin Mata da aka ware musu a Companin suna sallah Sai da suka dawo sannan ta shiga ta same shi kamar yanda ya buƙata, Zama tayi tana jiran ta ji mai zai ce mata, amma har cikin ranta tana jin wani yanayi kamar wani abu zai same ta, musamman yanda ta ji zuciyarta na beating natsuwarta na neman kufce mata cus kallon da yake mata, dalilin da yasa ta mayar da kanta ƙasa kenan domin ta kasa jure kallon nasa wanda ke faɗar mata da gaba Hanif shiru yayi ya zuba mata idanu yana tunanin ta inda zai fara, murmushi kawai yake yi a ransa yana jin daɗin kasancewar su a haka yana kallon kyakkyawar fuskarta, It took some time before ya buɗe baki ya kira sunan ta, Ganin ta ƙi ɗagowa shiyasa ya ci gaba da maganar sa cikin kwantar da murya da salon jan hankali, "Amrah, I know you will be surprised what will come out of my mouth now, ahmm... Duk da dai lokaci ya ja ina dakon sa a cikin raina ban samu na bayyana miki ba sabida ina buƙatar mu sake fahimtar juna sosai." Sai ya sake kiran sunan ta cikin wani yanayi tare da furta, "I can't hide it for a long time, now I have to tell you what I feel in my heart. I love you AMRAH! I love you from the bottom of my heart, I am telling you my truth." Weakly, she raised her head and looked at him, her heart beating very well, ta kasa ƙwaƙƙwaran motsi sai faman kokawa take yi da zuciyarta, yanda ta zuba mishi ido take a nan ƙwalla suka soma cika mata idanun sabida gani take yi kamar mafarki take yi While shi kuma tuni ya taso sabida ganin halin da ta shiga, sai ya zagayo ta wurin ta yana zama a kan table tare da kafa mata ido, cikin tsantsan gaskiyarsa da yanayin muryan tausayi yace, "Amrah ina sonki! Ina matuƙar ƙaunarki ba tun yau ba, na jima ina dakon soyayyar ki tun sanda na ganki, a yau ne nake ganin ya dace in fito da abun da ke cikin raina ko don in ji salama a cikin zuciyata; sannan in samu amsa gamsashshiya wacce zata faranta min rai, don Allah ki dube Ni ki faɗa min abun da ke cikin ranki a game dani, Ni ina sonki! Kuma auren ki nake son in yi Amrah." She never thought she would hear these words from him, that's why she was confused at the same time, cike da tsoro da mamakin sa take kallonsa, tana ganin bata kai matsayin da kamar Hanif zai tsaya a gabanta yana furta mata kalman so ba, to mai zata ce mishi? Wannan tambayar shiyasa ta kasa kataɓus kanta a ƙasa jikinta na rawa; matsananciyar kunya ta kama ta Shi kuma Hanif ya kasa jure shirun ta burin sa kawai ya ji amsar sa a gunta, don haka ya ci gaba da tausasa murya yana gaya mata irin ƙaunar da yake mata, kuma amsar ta kawai yake buƙatar ji a yanzu A yanda ya nuna damuwarsa da kalallametan da yake yi; ta rasa abun yi a wurin, ga kunya ga mamakin kalaman nasa da bata taɓa tunanin hakan ba, tabbas baza ta ce ba ta son Hanif ba, sai dai a yadda take bata taɓa kawowa a ranta zai iya sonta ba bare har kalaman soyayya ta shiga tsakanin su, tana da wani abu, bata ɗaura wa kanta abun da ta san ya fi ƙarfin ta; duk kuwa da abun da take ji a ranta ba takai kanta inda Allah bai kaita ba, A ganin ta Hanif ya wuce ya zo wurin ta ya ƙasƙantar da kansa domin neman soyayyarta, amma sai ga shi abun ya zo mata a bazata; a mugun bazata, wanda hakan ya saka ta a wani irin yanayi; sam ta rasa abun da yakamata tayi, ya fi ƙarfin tayi rejecting soyayyarsa, domin shi wani bango ne ko in ce rumfar da yayi musu mafaka a rayuwa, koda ba ta son sa baza ta taɓa ƙin amince masa ba, domin duk abun da ya nema a rayuwarta a shirye take tayi masa shi da iya ƙarfin ta, Hanif ba abun wulaƙanta wa bane a gare ta, bare dama ba ta ƙin sa, abu ɗaya ne ya raunata mata zuciya; sabida kasancewar ta naƙasashshiya mara galihu, Tuni ƙwallan da suka cika mata idanun sun soma ɗiga a saman kuncin ta, tayi shiru kanta a ƙasa ta kasa kula sa bare ta dakatar dashi daga sambatun da yake yi, Me zata yi masa ta saka mishi a rayuwa? Ta yarda cewa Hanif yana sonta; ta yarda da iya gaskiyarsa yake faɗa mata waɗannan kalaman, tabbas abun farin ciki ne a gare ta a ce kamar Hanif yana sonta, amma ba ita ya dace ya nema ba, Don haka sai ta ɗago kanta da sauri tana kallonsa, bakinta na rawa kamar zata yi magana amma ina ta gaza yi sabida ko tayi yunkurin yi sautin muryanta bazai taɓa fita ba Hankalin sa ya tashi da ya ga hawaye a saman kuncin ta, Before yayi magana sai ya ga ta tashi da sauri tana shirin fice wa, Take shima ya tashi ya mara mata baya yana shan gabanta, tare da kallonta cikin tsananin damuwa da ruɗun da ke barazanar tarwatsa mishi zuciya, don yanda ya ga hawaye a idanunta hakan ya saka mishi wasi-wasin rashin amincewar ta dashi, Shi yasa babu zato babu tsammani ta ga ya duƙa mata a gabanta yana rokon ta da faɗin, "don Allah Amrah ki bani amsar tambayana kar kibar wurin nan batare da kin amince dani ba, yanayin da na ganki ya saka min shakku a zuciyata, ko ba ki yarda da soyayyar da na furta miki bane? Kina ganin kamar ƙarya ne ko?" Girgiza kanta ta soma yi jikinta na rawa sabida ganin yanda ya duƙa mata, da sauri ta duƙa itama tana ƙoƙarin mishi bayanin, "ya tashi tsaye ba ta son ganin sa a haka." Hannunsa ya sanya yana ciro wayansa cikin aljihu da sauri, tare da miƙa mata yace, "ki min bayani a nan." Miƙa hannu tayi ta amshi wayan ta soma yin typing hannunta na rawa, duk alamun ruɗe wa ya bayyana a tare da ita, Tana gama wa ta miƙa masa wayan Shi kuma ya karanta ya gani before ya dube ta yace, "no bazan tashi ba har sai kin bani amsar tambayata, ina son in duƙa miki ne sabida ki amince dani, domin a yanzu nayi nisa da dakon soyayyarki ba na jin zan iya jure rashin ki." Hannu ta sa ta amshi wayan ta sake rubuta mishi, "ta yarda ya tashi zasu yi magana." Ganin abun da ta rubuta, shiyasa ya miƙe, itama yace, "ta taso su zauna." Babu yadda ta iya dole ta koma wurin zaman ta tana duƙar da kanta ta kasa cewa uffan, sabida jiran da yake yi tayi masa magana, wayansa na hannunta yana sauraron abun da zata rubuta mishi, Sai da ya sake mata magana before ta soma rubutun a tsanake zuciyarta na tsintsinke wa "Yaya Hanif, ba abun da zan iya saka maka dashi a duniyar nan ko me na baka, ko mai ka nema a gare Ni a shirye nake da in baka shi hannu bibbiyu ina mai farin ciki in bar bai saɓa wa mahaliccin mu ba, sai dai abun da ka nema a wurina a yanzu yayi ƙanƙantar da zan iya baka shi, kasancewata ina da wata tawaya da bazan iya baka farin cikin da kake so ba, ba Ni ya dace ka so ba, amma tunda ka buƙata a gare Ni zan baka ƙanwata Afra, zata fi dace wa da kai fiye da Ni, duk da haka gani nake yi ban kyautata maka ba domin ka wuce haka a gare mu, kayi haƙuri ka amshi Afra ƙanwata domin ita tana yin magana, bata da tawaya kamar Ni, baka dace da Ni ba, baza ka taɓa dacewa da Ni ba har abada, ba na son wata matsala a nan gaba." Shiru tayi tana kallon rubutun hawayenta na ɗiga a saman wayan, Lumshe idanunta tayi before ta ɗago ta miƙa masa wayan, sai da ya amsa sannan ta saka hannu ta soma share hawayen tana mai duƙar da kanta zuciyarta na mata wani irin ƙuncin da ta kasa gane dalili Shi kuma da ya gama karanta wa sai ya ɗago yana duban ta, fuskarsa ba walwala yace, "ba ita nake so ba ke nake so Amrah, idan har kin san cewa na wuce neman abu a wurin ki ban samu ba, to ki amince da soyayyata domin shine kaɗai abun da za kiyi ki faranta min, Ni na san ƙaddara kuma na san da cewan ke Kurma ce amma a haka nake sonki, ina sonki Amrah! Ke nake so ba wata ba, do you love me? you can marry me? Amsar ki nake buƙata yanzu." Ido ta zuba mishi, a wannan lokacin ta kasa ɗauke idanunta daga cikin nasa, zuciyarta na wani irin bugawa da ƙarfi kamar zata faso ƙirjin ta, wani irin ƙauna da zallan soyayyarsa ne ke mamaye a cikin zuciyarta, baza ta iya ce masa a'a ba, shiyasa a hankali ta gyaɗa mishi kanta alamun amince wa, yayinda tayi ƙoƙarin miƙe wa tabar wurin da sauri, Sai ta ji saukar muryansa cikin sautin dariyansa da ya bayyana farin cikin sa "I love You so much! I really love you! Thank you for trusting me. You are the only one in my heart, I love you My Amrah!" Kasa haƙura tayi lokacin da ta isa bakin ƙofan ta buɗe, sai da ta waiga ta kalle sa tayi masa murmushi; murmushin da ya sanyaya masa zuciya, before ta fice da sauri; itama tana jin farin ciki a zuciyarta wanda ta rasa daga inda yake fitowa Secretary da ya ɗago yana duban ta, mamaki yayi sabida ganin yanda ta fito da farin ciki amma kuma face ɗin ta ɗauke da hawaye, abun ya ɗaure masa kai shiyasa ya tambaye ta abun da ke faruwa? Amma sai Amra ta nuna masa babu komai ta kasa sanar mishi abun da ke faruwa, Sai ma ƙoƙarin kawar da tambayoyin da yake jero mata tayi, ta ƙi basa fuska ta mayar da hankalin ta kan aikin ta Dole shima ya hakura da jin ƙwaƙwaf tunda bazai samu abun da yake so ba, amma yana ji a jikinsa akwai abun da ke faruwa, ya daɗe yana mamakin yanda ta fito cikin office ɗin, time to time sai ya ɗago ya kalle ta yana sake mamaki da ganin yanda take murmushi ita kaɗai; kuma babu natsuwa a tare da ita, kamar ma bata a cikin tunanin ta sabida hannunta na kan computer tana latsa wa amma idanunta da hankalin ta ba sa kai. *** _____Ƙarfe biyar kamar yanda suka saba tashi, yau ma a haka suka tashi, Motansa Amra ta hau suka wuce, duk da bata so bin sa ba amma bata da yadda zata yi; baza ta iya zille masa ba A cikin Motan ma wani irin kulawa ya dinga bata yana furta mata irin tarin ƙaunar da yake mata, Duk kunya ya cika ta ta kasa sakin jikinta, rufe idanunta tayi da Hijabin ta kawai tana sauraron zantukan nasa waɗanda suke sanya ta nishaɗi da farin ciki A hankali yake tuƙa motan har suka isa gidan su Sabida kunya yasa Amra ta kasa tsaya wa, da sauri ta fice har da haɗa wa da gudun ta tabi lungun gidan su, Bata juya ba har ta shige cikin zauren gidan before ta dakata tana sauke numfashi, yayinda ta sanya hannu a kan ƙirjin ta tana jin yanda yake buga wa da ƙarfi, Yau tana cikin farin ciki, ina zata saka wannan farin cikin? Haƙiƙa yau Allah yayi mata kyautar da babu kamar ta a tarihin rayuwarta, Hanif tamkar haske ne a tare da ita, samun Hanif a matsayin Masoyinta tana ji a jikinta tabbas zata yi farin ciki, yana da kirki matuƙa, ta tabbata bazai taɓa wulaƙanta ta ba, Sai da ta jima a wajen before ta sanya kai ta shiga gidan, Sai dai lokaci ɗaya farin cikin nata ya gushe da ta tabbatar da abin da ke faruwa a gidan, Domin a cikin wani hali ta zo ta tarar da Mahaifiyarta duk da su Salma sun tafi Islamiyya, Damuwar da ta gani a tattare da ita har da hawaye shi ya ɗaga mata hankali, nan da nan ta tashi hankalin ta ta soma tambayarta abun da ke faruwa Ita kuma Mama sai ta kasa faɗa mata; sai ma tambayarta da ta hau yi, "tare da Hanif suke ne?" Ta bata tabbacin hakan da sauri tana bin ta da kallo cikin tashin hankali "Na manta ban sanar miki ba, ina son ganin sa amma na san yanzu ƙila ya tafi." Hannu ta ɗaga tana sake tambayarta abun da ke faruwa tare da faɗin, "mai Hanif ɗin zai yi mata? Sai ta kira sa a waya." Dakatar da ita tayi ta hana ta, tace, "ta bari ko zuwa gobe sai a kira shi." Duk da ta so ɓoye mata abun da ke faruwa; but haka nan ta zayyane mata zuwan Baba Jafaru da rashin mutuncin da yayi, duk da haka ba dukka ta faɗa mata ba tunda sauran ƴan uwan Baban nasu sun zo suma sun ci mata mutuncin ta uwa da Uba, sun yi mata zaga-zaga, sun kuma ce, "sun bata daga yau zuwa gobe ta tattara tabar gidan nan, ta zube yaran zasu iya riƙe su, kuma zancen Amra da Jabir tunda ya nuna yana so ko bata so sai ya aure ta, ƙaryan tsiya take yi bata isa ta hana shi ƴar uwansa ba." Shi yasa ta ɓoye mata tunda ta san Amra zata ɗaga hankalin ta yanzu ta shiga wani hali Duk da a yanzun ma kuka ta dinga yi sai da Mama ta tsawatar mata sannan tayi shiru, Ta faɗa mata, "babu wanda ya isa ya ƙwace mata su ko yayi musu wani abu in har tana nimfashi". *** _____Lokacin kafin Hanif ya koma gida; Baba Jafaru da ƴan sanda suka je gidan su suka yi sallama da mai gidan, Mai gadi ya je ya kira Dady suka fito tare, A nan ƴan sandan suka yi masa bayanin, "Baba Jafaru ne ya kawo musu ƙara a kan ɗansa da ya rufe mishi ɗa, yanzu haka case ɗin na hannunsu suna son su tafi da Yaron don a je a yi bincike." Dady yayi mamakin abun da suka faɗa, bai san wanne ɗansa suke magana a kai ba shi yasa ya tambaye su ya faɗa musu cewan, "Yaran nasa su uku ne, bai san wanne suke magana a kai ba?" Ɗaya daga cikin ƴan sandan tunda su ne suka je suka kama su Jabir, ya san Hanif sosai; kuma a yanzu Ogansu ne yace, "su zo su taho dashi tunda Baban Yaron ya kawo ƙara, gwara su kira shi a yi zama a ji dalilin abun da suka yi masa." Shine yayi masa bayanin, "Hanif ne ya saka su suka kama ɗansa, to shi yanzu ya shigar da ƙara ne sai an amsar musu haƙƙin su." A tunanin Dady ma SHAREEF zasu ce tunda shine ya fi zaton za a iya wannan rigiman dashi, bai taɓa kawo Hanif bane, but jin hakan sai yace musu, "yanzu Hanif ba ya nan yana wurin aiki, amma zasu iya tafiya tare don ya ji ainihin abun da ake tuhumar ɗansa dashi, da kuma dalilin kama wa mutumin ɗansa." Tunda hankalin sa ya tashi gaskiya shiyasa ya nuna zai bi su kawai, in da hali shi ya kashe case ɗin Baba Jafaru bai so hakan ba, ya so Hanif ɗin za a wuce dashi, baƙin cikin sa ma da ya ga ɗan masu kuɗi ne tunda babu wanda bai san Alh. Ahmad Sama'ila a wannan garin ba, sunan shi yayi fice gaskiya, yana ɗaya daga cikin masu kuɗin Garin Kano, wanda ko baka sanshi ba zaka ji sunan shi a baki in ana faɗan masu hali, ko kuma ka samu taimakon da yake yi wa jama'a ko baka sanshi a fuska ba, Shiyasa Baba Jafaru bai so ba don ya san za a iya tauye musu haƙƙi tunda da ɗan masu kuɗi zai ja zancen, amma duk da haka bai karaya ba haka suka tafi a ransa yana shirya kitimurmuran da zai yi a station din, dole sai an hukunta su har su Amran, a kan ɗansa ba abun da bazai yi ba Su Momy da suke Falo sun ji shiru bai dawo ba daga yin sallama, ga shi har ƙaran Mota suka ji ya ɗauka ya fita, Shi yasa hankalin Momy bai kwanta ba since mai gadin tun farko ya faɗa musu ƴan sanda ne, Waya ta ɗauka ta kira Dadyn tana tambayarsa, Shine ya faɗa mata abun da ke faruwa, Dalilin da yasa gaba ɗayan su hankalin su ya tashi har SHAREEF da ke kwance saman three seater, duk abun nan bai yi motsi ba idanunsa a rufe yana faman tunanin da ya zame mishi jiki, Kyakkyawar fuskar nan nasa har ta rame ta faɗa kamar ba shi ba, ga ƙasumba da ya ajiye yayi yawa duk ya sauya mishi kamanni sabida rashin gyara, a kwanakin nan sam ba ya jin dad'in jikinsa, ko karsashi ba shi dashi shiyasa yau da ya tashi da ciwon kai ya ƙi zuwa wurin aikin, duk da har ya shirya zai je amma ya haƙura da zuwa, Daga shi sai short trouser da farin singlet a jikinsa, Jin abun da ke faruwa shine ya tashi zaune yana tambayar Momy madaidaitan idanunsa duk sun shige sun sake fari fat kamar madara Tana cikin sanar mishi ne Hanif ya shigo gidan Shi kansa SHAREEF yayi mamakin cewa da aka yi wai Hanif ne aka zo tafiya dashi, Yana shigowa kuwa tun kafin kowa yayi magana shi ya fara mishi magana, ba tare da ya bari an amsa mishi sallaman nasa ba, yace, "Hanif wai meke faruwa ne? Mai ka yi wa ƴan sanda suka zo tafiya da kai?" "Ƴan sanda kuma?" Hanif yayi maganar cikin mamaki sabida har ga Allah ya manta abun da ya faru da safen Momy tace, "eh mana, yanzu suka tafi da Dadyn ku a kan sun zo tafiya da kai, shine ya bi su don ya ji ba'asi.." Shiru yayi da mamaki kwance a kan fuskarsa har yanzu, sai kuma cikin lokaci abun da ya faru ya faɗo masa yace, "oh! Na tuna, to ai Ni ne na saka aka kama min wani ɗazu da safe..." Saurin katse sa Momy tayi tace, "a kan me to? Mai yayi maka Hanif; Kai da baka da rigima kuma?" Zama yayi gefen Sadiq yana ajiye Jakarsa tare da faɗin, "Momy wasu ya so cin musu zarafi shine dalilin da yasa na ɗauki mataki, domin Yaron irin waɗannan ƴan iskan nan ne ƴan shaye-shaye, don haka zan wuce can kawai in ji abun da ke faruwa." Cikin rashin jin dadi Mom ta dube sa da cewa, "to ina ruwanka Hanif? Meyasa zaka shiga abun da bai shafe ka ba?" "Mom na san baza ki hana Ni aikin alkhairi kamar wannan ba, sannan ma yarinyar na santa tunda a karkashina take aiki, su marayu ne suna bukatar taimako, har cikin gidan su yake shiga yana cin musu zarafi, kuma yana son ya lalata musu yarinya, gaskiya bazan iya bari ba koda ban sansu ba bare akwai alaƙa a tsakanin mu." Jikin Momy yayi sanyi, sai tace, "haka ne, gaskiya ka kyauta da ka taimaka musu, amma tunda ka fi sanin abun da ke faruwa yakamata ka bi Dadyn ku tunda kai aka zo ɗauka, inyaso sai ku san mai ke faruwa." "Haka ne Mom bari in je." Yayi maganar yana miƙe wa da sauri SHAREEF shima miƙewa yayi yace, "jira Ni bari mu wuce tare." Sai ya juya ya koma upstairs ya je ya saka kaya, riga da wando ne ƙananu, sai ya saka ƙaton cumbas a ƙafafunsa kalan blue t.shirt ɗin da ke jikinsa, Sauko wa suka yi suka wuce a tare, duk da Sadiq ya so bin su amma Hanif ya hana shi. [31/03, 4:33 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE10* _____When Hanif arrived at the police station, they found them in the DPO office, Lokacin an je fito da su Jabir kamar yanda DPO ya bada umarnin a kawo su don a yi komai a gaban kowa, Yana cikin tambayar Dady zuwan Hanif ɗin, A lokacin sai ga su sun zo station din, wani Constable ya shigo yana sanar da DPO, shine ya bada umarnin a shigo da su A tare suka shigo cikin office ɗin, Hanif na gaba SHAREEF na biye dashi a baya, Bayan sun gaisa DPO yace, "su zauna." Ya nuna musu wurin zama kafin daga bisani yace, "yanzu dai ga kowa ya hallara tunda ga wanda muke nema nan, amma duk da haka sai an kira Mahaifiyar yarinyar da ita kanta yarinyar sun zo nan sannan a tattauna abun da ke faruwa, Alh. Ahmad don da kai a cikin zancen nan shiyasa gwara a nemi maslaha mu ji ta inda matsalar take, hakan zai fi." Dady yace, "gaskiya ne DPO, to ina ga za a iya kiran su ai babu damuwa." Kafin DPO yayi magana ma; Hanif yace, "zai je ya taho dasu in babu damuwa." DPO ya ba shi dama sannan ya tashi ya tafi. *** _____Almost fifteen minutes sai ga Hanif ya dawo tare da Mama da Amra, A tare suka shigo suna biye dashi a baya Sai da DPO ya nuna musu wurin zama sannan ya fara magana da faɗin, "to wadannan Yaran su ne waɗanda Hanif yasa aka kamo su bisa zuwan su gidan Matar nan suna ƙoƙarin cin zarafin su, koma in ce sun ci zarafin su har suka yi ƙoƙarin fasa mishi Mota, ASP ɗin da suka tafi kwaso su shi yayi min bayani, sannan har mun buɗe file a kansu, amma kuma sai Mahaifinsa yanzu ya zo mana yana kawo ƙaran shi Hanif ɗin a kan saka wa a kama mishi Yaro, kuma maganar da yayi a nan cewan shi Hanif yana neman lalata ƴar ɗan uwansa, wanda hakan ne yasa Yaronsa Jabir ya nemi ya ɗauki mataki tunda Budurwansa ce wacce zai aura, dalilin da yasa aka kama su kenan, to Ni kuma ganin Hanif shi ya fara shigar da ƙaran, dana bincika sai na gane ɗanka ne shiyasa nace to a kira min shi don a yi wannan zaman a samu maslaha, that's why ban bar maganar wurin ASP ba. Yanzu ina son in ji na bakin kowa tunda ga yarinyar ga mahaifiyarta." Sai ya dubi Amra yace, "ta kanki zan fara, mene ne tsakanin ki da shi Hanif ɗin?" Mama ne tayi saurin yin magana da faɗin, "Yallaɓoi ita kurma ce, amma zan iya faɗan abun da ke tsakanin su." "Ayya, ok to. go ahead, ke za ki iya magana ai. Babu damuwa." Sai da Mama ta kalli inda Baba Jafaru yake, sai faman muzurai yake yi yana tsuke fuska, cikin baƙin ciki da tsanarsa take cewa, "Yallaɓoi abun da ya faɗa mutumin nan ba gaskiya bane, domin kuwa da shi da ɗansa basu da wata alaƙa damu illa na kasancewarsa ɗan uwa wurin Mijina, kuma tun sanda ya rasu komai ya ƙare na alaƙar mu, dalilin kuwa da suke bibiyar mu ɗansa ne yake son wulaƙanta min yarinya, domin ya sha neman ta yana son lalata ta Allah bai ba shi nasara ba, ba tun yau ba na sha zuwa wurin mahaifinsa ina faɗa masa ya ja kunnen ɗansa amma ya ƙiya sabida yana goyon bayansa a cewar sa babu abin da dansa zai aikata, Shi kuma Jabir koyaushe sai ya zo gidan mu yana cin mana mutunci, babu cin kashi da zagin da bai yi mana ba, to yau a gaban Hanif aka yi komai tunda ya zo ɗaukar ta su je wurin aiki, shine ya shiga tsakani ya hana sa aikata ƙudirin sa a kanta, domin so yayi ya tafi da ita ta ƙarfi da yaji, shi kuma Jabir ya dinga zagin sa kuma yace sai ya ɗauki mataki a kansa, hankalina ya tashi tunda na san Yaron bai da mutunci ɗan shaye-shaye ne komai zai iya yi tunda ya furta muggan kalamai a kan Hanif, to lokacin da suka dawo da Abokansa ashe shi ya kira ƴan sanda, shine suka tafi dasu, Amma shi yayi komai ne don martaban ƴata, don Allah DPO a taimaka a ƙwatan ma ƴata ƴancin ta a raba ta da wadannan azzaluman mutanen, domin suna shiga hakkinta, Jabir ya takura mata, ya shiga rayuwarta da yawa har dukan ta yake yi don kawai yana ganin bamu da ƙarfin da zamu iya ja dashi, sannan yana da ɗaurin gindin mahaifinsa, amma wlh babu zancen aure a tsakanin su kawai mugunta ne da cin zarafin da yake mata a kan dole sai ya aure ta, kuma ita ba ta son shi." Ta ƙare maganar tana hawaye While itama Amra tuni ta kwantar da kanta a jikin Maman tana nata hawayen; har da su shashsheƙa Dukka babu wanda bai ji tausayin su ba, musamman ma Hanif da ransa babu abin da yake yi sai suya da tafarfasa, zuciyarsa na masa zafi kamar ya miƙe ya shaƙo Jabir ɗin SHAREEF kuwa yana zaune ne yana sauraron abun da ke faruwa, baza ka taɓa gane yanayin sa ba tunda shi mutum ne da ba ya shiga abun da ba ruwan sa, mamaki ma yake yi har yaushe Hanif ya san yarinyar da yake zuwa ɗaukan ta since bai taɓa sani ba, to meye haɗin sa da irin ƙasƙantattun mutanen nan; kuma Kurma ma? Idanunsa a kan Jabir ne sai bin su da kallo yake yi ba ya ko ƙyafta wa DPO ne yace, "Malam Jafar kaji abun da Mahaifiyar yarinyar ta faɗa, amma kuma kai ka bamu bayanan da ya saɓa haka, ko kana da bakin maganar da zaka kare kanka?" Shi kansa bai san cewan hakan zata faru na kiran da DPO yayi musu ba, duk da kunyar ƙaryan da yayi amma hakan bai sa ya sauya daga maganar nasa ba, tare da furta, "tun farko ɗan uwansa Abubakar ya ba ɗansa auren amra, dama tun kafin ya rasu sun ajiye Maganar haɗa auren zumunci, sauran yan uwansa ma sun san da zancen. Amma yanzu ita Shafa tana son ƙaryata shi ta ci mishi mutunci don an zo gaban hukuma, yaran nan fa nawa ne ina da damar da zan iya amsar su a yanzu ma ba sai anjima ba, don haka muddin bata amince da maganar nan ba to zasu dawo hannuna tunda mu ne dolen su." Girgiza kai Dady yayi sabida mamakin furucin Baba Jafaru, ga shi kamar babban Mutum amma ashe irin dattijan nan ne da basu san abun da yakamata ba, Don haka ya riga yin magana da fadin, "Gaskiya ka bamu kunya, ga ka babban Mutum amma son zuciya yasa kana ƙoƙarin tauye musu hakkin su, kuma ƴaƴan yan uwanka fa, ko wani ka ga zai ci musu zarafi ai sai inda ƙarfin ka ya ƙare, shin ana so dole ne? Sannan idan ka raba uwa da ƴaƴanta mene ne riban hakan a gare ka?" DPO yace, "to wanne riba kuwa ban da son zuciya irin na mutanen mu na wannan zamanin? Ai Alhaji irin wannan cases ɗin da yawa ana kawo mana su a offices, mutane dai son zuciya yayi musu yawa, abun tausayi ma ga ta yarinyar babu bakin magana; wacce abar a tausaya mata ne, amma yabar ɗansa irin wannan mara sa jin yana ƙoƙarin ɓata mata tarbiyya, bai ɗauki mataki ba tunda nasa kawai ya sani, ƴaƴan ɗan uwansa ba nasa bane, idan da ace mahaifinsu na nan kun isa ku ci musu mutunci irin haka? To gaskiya Malam Jafar a wannan wurin ku ne da laifi, don babu inda aka ce a yi wa yarinya auren dole don kawai kuna son haɗin zumunci, meyasa bazai nemi yardan ta ba amma sai ya nuna mata ta ƙarfi, kuma kana gani amma baka dauki mataki ba? Wlh ka bamu mamaki, don haka baza mu lamunci wannan abun ba, tunda mu ne masu ƙwato wa Al'umma mara su galihu kamar su haƙƙin su; daga yau tunda maganar ta zo gabanmu zan muku iyaka da su, ku ne dai dolen su tunda babu yanda za a yi a raba ku dasu, amma kar ku soma ku sake yunkurin musu auren dole in har bada amincewar su ba, sannan kai kuma." Ya nuna Jabir da yake tsaye jere da sauran Abokansa suna zazzare ido da cije baki, "duk rashin kunyar ka a nan zamu gyara maka zama ne, in har ka sake ka ƙara laifin da aka kawo ka nan, wlh summa tallahi a cell zaka ƙarike rayuwarka, daga yau babu kai babu yarinyar nan tunda ta nuna ba ta sonka, in har suka kawo mana ƙara a kan ka sake shiga sha'anin su; zaka ga yanda zamu yi da kai, mutanen banza mutanen hofi, gaba ɗaya kun ɓata rayuwarku da shaye-shayen banza, kuna aikata abin da ba shine ba babu tsoron Allah a zuciyarku, ko kuyi hankali ko mu mu koya muku hankali. Don haka Ni yanzu zan sallami kowa bisa sharaɗin kai Malam Jafar da ɗanka baza ku ƙara cin mutuncin wadannan bayin Allan ba, ku ƙyale su suyi rayuwarsu cikin salama, Ni dai bazan yanke alaƙar ku ba tunda ku ne dangin su, amma suna da right na zama a duk inda suke so, to kwana nawa ne ma yarinyar zatayi aure ta bar ku?" "Gaskiya ne wannan maganar naka DPO, and Ni ina ga tunda abun ya zama haka, yawanci irin wannan abun yana faruwa ne a kan rabon gado ko wani abu da mahaifi ya tafi ya bar shi, tunda abun haka ne zan ba marayun nan gidan da zasu koma kyauta, halak malak; wanda ba sai sun kori mahaifiyar ko sun ci zarafin ta ba, sai ta koma can ta zauna hakan za a fi samun sauƙi." Baki DPO ya washe yana cewa, "Masha Allah Alhaji, gaskiya idan ka yi hakan ka kyauta kuwa, Allah ya ƙara buɗi da lafiya, tabbas ka taimaki marayun nan, thank you so much!" Nan fa itama Mama ta soma kwararo masa addu'o'in cikin tsananin farin ciki, Daga ita har Amran bakin su a washe da hakan zai nuna sun ji daɗin kyautar da aka yi musu Don shi kansa Hanif ba ƙaramin murna yayi ba, wanda ya san dama ba sabon abu bane wajen Dadyn su, yayi ma wasu banza ma bare waɗanda ya gansu a cikin matsala Dady kuwa yayi hakan ne sabida ya tausaya musu matuƙa, tunda ya san matsalar irin waɗannan dangin Uban; duk abun da zaka ga suna yi duk saboda gado ne, domin shi yake jawo hakan, kamar yanda Baba Jafaru ya faɗa ne ya san cewa zasu iya koron Uwar su gaje gidansu da komai nasu har Yaran, amma idan ya tallafa musu da gida hakan ba ƙaramin taimaka musu zai yi ba, gwara su koma can da zama zai fi, shiyasa yayi maganar cewan, "Hanif zai kawo musu takardar gidan gobe sai su tashi su koma can, kar su jingirta ko kaɗan." Mama ta amsa mishi da to cikin farin ciki har yanzu tana zubar da hawaye; wanda ya koma na farin ciki Daga nan yayi musu sallama ya tafi, Shima SHAREEF miƙewan yayi ya bi bayan Dadyn su tunda bai ga amfanin zaman shi a wurin ba, Aka bar Hanif kaɗai a wurin While shi kuma DPO ya sake jan kunnen su Jabir tare da Abokansa, kuma yace, "an yafe musu wannan laifin ne kawai don sun ci albarkacin mutanen nan, amma da basu isa ya sake su ba." Rubutu yayi ya basu suka saka hannu, har Baba Jafaru da baƙin ciki da haushi ya cika sa kamar yayi hauka, Itama Mama ta saka hannun sannan DPO ya sallame su, Dukkan su suka fita a tare, Hanif ya ja su Mama suka wuce gida A Mota sai sanya mishi albarka take yi har da kukan ta, farin cikin ta ya gaza ɓoyuwa, sai faɗa masa take yi, "ya ƙara ma mahaifinsa godiya don Allah." Hanif kuwa murmushi yayi yace, "Mama babu komai, Dady yana yi wa da yawan mutane masu matsala irin wannan, don yayi muku kyautar gida ba komai bane, zuwa gobe sai ku shirya da wuri zan zo in tafi da ku tare da takardun gidan, ba sai Amrah ta je aiki ba nima bazan je da wuri ba, zuwa ƙarfe goma zan zo mu wuce." Dad'i kamar ya kashe su, farin cikin su ya gaza ɓoyuwa, Ita kanta Amra haƙoranta sun ƙi rufuwa don farin ciki, yau dai matsalar su ta kau duk a sanadin Hanif, shiyasa a ranta wani irin farin ciki da ƙaunarsa ne gauraye kamar ta samu bakin da zata iya furta masa ƙaunar da take masa; gami da godiyarta gare shi Sai da ya kaisu lungun gidan su sannan ya sauke su, Sallama kawai suka yi ya tafi, duk da yana son ganawa da Amra amma ya gaza tsayar da ita, kasancewar magriba tayi a time ɗin ma, ana ta ƙwalla kiran sallah Ita kanta tayi tunanin zai tsayar da ita ne, amma kuma tunda ta kalle sa suka haɗa ido ta ɗauke kanta sai zuba murmushi take yi, cike da kunya da tsananin soyayyarsa, Tana jin godiyar da Mama take masa amma ita bata da bakin magana, Sai da ya ja motan zai tafi before ta sake kallonsa duk da ba ta ganin sa, Sai da motan tayi nisa before ta bi bayan Mama suka wuce gida, Suna shiga bata tsaya mayar da hankali a kan su Afra da suka dame su da tambayoyi ba, kai tsaye dakin su ta wuce ta ɗauki wayanta ta soma rubuta text, domin abun da zuciyarta ta kitsima mata kenan, ba ta son ta ƙara jinkiri bata bayyana masa godiyarta a gare sa ba, don haka ta tsara mishi tausasan laffuza masu ɗaukan hankali da ita kanta bata san ta iya su ba, fuskarta ɗauke da murmushi haka take typing ɗin cikin yanayin shauƙi, daga karshen ta rubuta mishi tana matuƙar ƙaunar shi, Sai da ta sake karantawa before tayi sending ta tura masa zuciyarta wasai, text ɗin yana tafiya ta rungume wayan idanunta a rufe tana dariya mai sauti cikin farin ciki. *** _____A hanya Hanif ya ji ƙaran shigowar text ɗin, bai ɗauka ba sabida tunanin da ke tare da shi, hankalin sa gaba ɗaya yana ga tunanin Amra shi kansa sai zuba murmushin yake yi cike da tsananin ƙaunarta, Allah ya ɗaura masa son wannan baiwa nasa, wanda bai taba tunanin hakan ba, Sai da ya iso bakin gidan su before ya dawo hayyacinsa, horn yayi kusan sau uku before mai aikin gidan ya rugo aguje ya buɗe masa gate ɗin, don a lokacin Mai gadin ya kewaya, shi kuma mai aikin yana wurin yana alwala, sai yayi saurin ƙarisa alwalan ya je da gudu ya buɗe masa Bayan yayi parking bai tsaya ɓata lokaci ba ya fito ya saka wayan a aljihun sa ya nufi cikin gidan da sauri, A nan falo ya ci karo da su Dady suma sun fito zuwa masjid, Da sauri ya ƙarisa toilet ɗin Falo ya ɗaura alwala ya bi bayansu, Sai da aka yi sallan isha'i sannan suka dawo gida gaba ɗaya Sai lokacin Momy ta nemi ta ji abun da ya faru a station din, Dady ya zayyane mata komai, Ita kanta ta tausaya musu matuƙa tare da Allah wadai da masu hali irin na Baba Jafaru; don kowa ya san son zuciya irin na wasu mutane da ke faruwa a yanzu, mugunta da cin zalun marayu yanzu ya zama ruwan dare, Kuma ikon Allah a cikin su babu wanda yayi zargin akwai wata alaƙa tsakanin Amra da Hanif, baya ga na wacce take aiki a ƙarƙashin sa basu kawo komai ba, musamman da suka ji cewa yarinyar Kurma ce, kawai sun yi tunanin maybe taimaka mata yake yi har ya je ɗauko ta, ko kuma sun saba tunda ma'aikaciyar sa ne, bare shi mai tausayi da sanin yakamata, ko kusa basu taɓa kawo Hanif zai so ta ba, Shiyasa tuni sun sauya zancen sun koma hiran su daban Har suka yi dinner Hanif bai duba wayansa ba tunda hankalin sa yana wurin hira, Sai da Mahmud ya kira sa yana sake tuntuɓan shi a kan maganar da suka yi ɗazu, da kuma saƙon da ya tura masa a WhatsApp, Shaf ya manta wlh, shiyasa da sauri ya kashe kiran ya soma duba wayan, a nan ya ci karo da saƙon Amra da ta tura mishi ta text messages, har zai wuce sai ya ga sunan ta ne that's why ya shiga yana karanta wa, Abun farin ciki bakin sa ya ƙi rufuwa don dad'i Dady da ke gefensa shi ya soma kula da shi, shiyasa yace, "my Son lafiya dai? Me kake kallo haka kake wannan fara'an?" "Dad babu komai, wani saƙo ne mai muhimmanci da aka tura min, amma bari in je ɗaki Goodnight ina da aiki." Yayi musu sallama ya wuce da saurin sa, Ɗaki ya koma zuciyarsa na masa wani irin dad'i, musamman da ya ji kalman son da ta furta masa, ji yake yi tamkar ya shiga wayan ya je ya haɗu da ita, wayyo! ina ma tana magana ya kira ta ya ji muryanta? Amma duk da haka zama yayi ya tsara mata nashi text ɗin tare da nuna mata farin cikin jin kalaman ta, Yana nan zaune yana jiran amsarta don babu abun da yake bukata da ya fi wannan, don haka tuni ya sake manta wa da duba WhatsApp ɗin sa; ya mayar da hankali kan saƙon Amra da ta sake turo masa, Daga haka fa sai suka ɓige da chart suna bayyanawa junan su irin ƙauna da begen da ke tare da su Sai da SHAREEF ya shigo ɗakin before Hanif ya tuna da zancen Mahmud, Sai fa lokacin ya shiga WhatsApp din ya buɗe saƙon, Video ne shiyasa ya kira SHAREEF yana faɗa masa, "Mahmud ya samo wani evidence tun ɗazu ya tura masa, da alamun an dace yanzu." Jin haka yasa SHAREEF ya dawo gefen sa ya zauna suka fara kallon videon Kamar yanda Mahmud yayi ma Hanif bayani ne ɗazu, akwai wani hotel kusa da Companin da suke gina wa, to bayan zuwan su Mahmud jiya sun fita da wani Abokinsa ya je raka sa hotel din tunda a nan ya sauka, suna cikin zanta wa sun fito waje suna maganar building ɗin da suke aiki akai, since daga wurin suna hangen ginin kasancewar yana opposite da hotel ne, kawai sai wannan tunanin ya faɗo wa Mahmud, cikin ƙanƙanin lokaci ya tuna ai hotel din nan akwai Cameras, mai zai hana su bincika ƙila za a dace a samu wani evidence na gobaran da ya faru, don dama har lokacin suna nan suna fama da neman hujja amma sun kasa samu, abun na ransa kuma sai tunanin nan ya faɗo masa, Dalilin da yasa yayi sallama da Abokin nasa kenan, bayan ya wuce shi kuma sai ya tafi wurin ma'aikatan hotel din ya nemi ganin Managern su, Allah cikin ikon sa duk da ya ba shi bayanin abun da yake so, amma sun ƙi ba shi goyon baya sai da ya basu cin hanci, sannan aka duba Cemaran da ke side na building, Mahmud yana da tabbacin za a iya samun wani abu tunda gobaran da yammaci ta afku, Kuma da aka duba na dai-dai ranan da gobaran ta faru, exactly sai ga shi an ga wasu mutane biyar da suke ta zirga-zirga a ranan, tun daga safe har yamma, sai kuma aka ga sun zagaya ta wani ɓangare sun haura ba tare da sanin masu gadin wadanda suka tafi yin sallan la'asar ba, Videon ya nuna sun jima a ciki sannan aka fara ganin hayaƙi ya soma ci, Abun da ya ɗauki hankalin mutane da masu gadin da suka rufta ciki don ganin mai ke faruwa, Nan fa suma jama'a suka hau hatsaniya suka mara musu baya, Babu jimawa sai ga su sun fito mutanen da Mahmud yake kyautata zaton su suka haddasa gobaran, domin sai a lokacin ya ga fuskar sani a cikin su, ya taɓa ganin ɗayan su da ya taɓa zuwa Companin su Hanif ya zo wurin Shuraihu, tabbas tare ya taɓa ganin su Wannan bidiyon shi Mahmud ya ɗauka ya tura ma Hanif bayan ya soma mishi bayani, tare da ce mishi, "ya shiga kawai ya kalla sai ya kira shi ya ƙara mishi bayani." To kuma hankalin Hanif ya ɗauke sanadin bayyana soyayyarsa wurin Amra bai duba ba, Shima kuma Mahmud bai kira sa ba don shima bai samu lokaci ba, sai yanzu da ya kira sa ya ƙara tuntuɓan sa since ya ji shiru bai kira ba, yace masa, "anya kuwa ya duba videon da ya tura masa?." _Ramadhan Mubarakh Masoyana, fatan kuna lafiya? Allah ya amsa ibadanmu ya hana mu ƙishin banza._ [31/03, 9:20 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE11* _____This video that they saw, they were very happy, ko banza yanzu sun samu hujja, Musamman SHAREEF yayi farin cikin ganin bidiyon nan, alamu ya nuna zai yi nasara a kan su Alhaji Inuwa, kwana kusa zai nuna musu ainihin wane ne shi, domin duk yanda suka kai ga wayon su; zasu girbi abun da suka shuka, asaran da suka sanya su ya ɗauki alkawarin sai sun biya su, Take ya kira Mahmud ɗin yana sake tambayarsa abun da ya faru Nan yayi masa bayani har mutumin da ya sani a ciki, wanda ya taɓa ganin su tare da Shuraihu a nan Company, kuma da alamu suna da relationship mai ƙarfi "Ok duk yanda za a yi gobe ka dawo Mahmud, kabar su PA a nan ka dawo sabida ka binciko mana inda Mutumin nan yake, before mu danƙa komai a wurin ƴan sanda dole muna bukatar hujja, sai mun saka su sun yi magana we will get proof and then we will take it to the police, idan wannan guda ɗayan ya zo hannun mu sauran ma zasu zo." Mahmud yace, "ok whatever you say it will be done, na san bazai bani wahalar nemowa ba insha Allah, zuwa gobe ina kan hanya." Bayan sun gama wayan; Hanif da ke sauraron su yace, "No bro, meye zai haɗa mu da aikin da yakamata police ne zasu yi? Ni ina ga idan an kama su just mu miƙa su wurin hukuma, a wurin su zasu yi bayanin waɗanda suka saka su, amma wannan aikin ba hurumin mu bane." Dubansa SHAREEF yayi yace, "bazan yi irin wannan saken ba Hanif, baka san yanda ƙasarmu ta lalace ba ko? Dole sai na samu ƙwaƙƙwaran hujja a hannuna before in miƙa su wurin ƴan sanda, don gudun samun matsala, waɗannan hatsabiban mutanen komai zasu iya yi." Shi kansa Hanif ya fahimce sa, shiyasa ya gyaɗa kai yace, "well, hakan za a yi kuwa, to shikenan Allah ya bamu Sa'a a kansu." Daga haka suka ci gaba da tattaunawa a kan maganar, har suka gama shirin su na kwanciya suka kwanta. *** _____Zuwa washe gari ƙarfe goma Hanif ya tafi gidan su Amra, domin ya kaisu gidan da Dady ya ba su While SHAREEF tun safe ya wuce wurin aiki, Tare da tsumayen dawowan Mahmud Shima dayake ya bugo sammako, kafin sha biyun rana ya shigo Kanon, Direct Companin ya wuto suka haɗu da SHAREEF, Sai da suka tattauna before ya wuce gida yayi uzurin sa, Daga nan fa ya soma bincikar yanda zai yi ya ga mutumin, Farko Companin Alh. Inuwa ya soma zuwa, cikin dabara ya soma bincika wa ko Allah zai sa ya haɗu da shi, kasancewar ya san a nan Shuraihu yake aiki shiyasa yake taka-tsan-tsan kar su haɗu, Bai wani samu abun da yake nema ba, dole ya koma Companin Honourable Ja'e can ma ya gama shawagin sa, Daga karshe ya kira SHAREEF suka yi magana da shi Shi ya ba shi shawaran, "ya riƙa bibiyan Shuraihun dole zai iya ganin su tare." Sannan ya faɗa masa, "ya shiga WhatsApp yana nan ya tura masa hoton mutumin wanda aka yi editing a videon, zai taimaka masa." A taƙaice dai ranan ta wuce Mahmud bai ci nasaran samo mutumin ba, Haka ma washe gari ya ɗaura da neman sa, babu inda bai je ba don ya samu damar da zai samo shi, a Companin Alh. Inuwa ya wuni yana bibiyan Shuraihu ko zai dace, Ganin har yamma tayi dole yayi kasada ya samu mataimakin Shuraihu a cikin sirri ya faɗa masa abun da yake so yayi masa, tare da yin masa alkawarin kuɗaɗe masu yawa Bayan ya nuna masa hoton mutumin, sai ya faɗa masa, "ya sanshi, amma bai san inda yake zaune ba, ya ba shi nan da anjima cikin dare ko gobe zai iya binciko masa komai a kansa." Mahmud ya ji daɗi yanda mataimakin Shuraihu ya amshi tayin sa bai nuna ja ba, don haka ya tafi yana saka ran dacewa, bai sanar da su SHAREEF ba don ya fi so sai ya kawo masa bayanan before ya faɗa musu nasaran da aka samu. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆       _____Yau Haseena ta dawo hutu, kasancewar tun bayan tafiyan da tayi after an ɗaura musu aure da SHAREEF, bata sake zuwa ƙasar ba, sai wannan lokacin Driver da Haajara suka je ɗauko ta, Abun mamakin yanda Haajara ta ga ƴar uwan nata ta sake sauya wa, kamar ba ita ba, gaba ɗaya tayi wani irin haske tayi jazur kamar jini zai fita a jikinta, dama tun farko Haseena tana shafe-shafe wanda hakan ne ya mayar da skin ɗin ta fara, but yanzu man da ta sauya ga gyara da take yi wa jikinta; ta ƙara sauya wa sosai, don ko SHAREEF da yake jawur idan ya tsaya a gabanta sai ya dishe, har da hujin hanci tayi irin na Nana, sai dai nata guda ɗaya ne kuma bata yi a baki ba Baki kawai Haajara ta saki tana kallonta, musamman yanda ta ga ta zuba zobuna a hannayenta sai shining suke yi kamar na zinare, ga farata a yatsunta masu tsayi sun sha kala, riga da wando ne a jikinta matsatstsu tamkar ba ƴar musulma ba haka ta koma, don har kanta ta bari a buɗe ta sha gashin attachment maroon colour, Kasa haƙura Haajara tayi tace, "wai Aunty Haseena anya kin ga shigan da kika yi kika taho nan? Kinga yanda kika koma kuwa?" Wani kallo ta watsa mata tana faman taunan chewing gum da ke bakin ta, sai wani ƙaras-ƙaras take yi kamar wata ƙasurgumar karuwa, Take ta shige cikin motan da aka zo daukar ta, ta ƙame a back sit ƙafa ɗaya kan ɗaya tana faman latsa tafkekiyar wayan da ke hannunta Motan Haajara ta shiga kusa da ita, sannan drivern ya ja motar suka tafi, since tuni ya zuba Jakar kayanta a Boot Duban ta Haajara ta sake yi bakin ta ya ƙi rufuwa don mamakin yanda ƴar uwan nata ta koma, ko ita da take bala'in son ƙananun kaya tun farkon ta, baza ta iya saka kayan da Haseena ta sa yanzu ba, bare har ta taho tun daga wata uwa duniya ta zo ƙasar su mutane na kallonta a haka, domin kayan da ta sanya dasu da babu duk ɗaya don bata ga amfanin saka su ba a yanda suka fitar mata da halittar jikinta, uwa uba yanda tayi mugun ƙiba komai na jikinta yayi ɓul-ɓul gunun sha'awa, koda gani Hutu da jin daɗi sun ƙara bayyana a tattare da ita, "Aunty Haseena, meyasa kika taho a haka bayan kin san nan ƙasar tamu daban da can inda kike? Idan kina wannan shigan a can bai kamata ki taho a haka ba, don wlh idanun mutane sai sun yi yawa a kanki, sai kin gummace ba ki taho a haka ba, bare kin san mutune ba a iya musu..." "Please shut your mouth, you are bothering me with this nonsense of yours." Ta jefa mata harara Tura baki Haajara tayi tana cewa, "ai gaskiya na faɗa Aunty Haseena." "To ki ci gaba da maganar, I will annoy you now." Ta ja tsaki tana ci gaba da latsa wayan da ke hannunta, face ɗin ta babu walwala wacce ke tattare da tsananin damuwa; sakamakon abun da suke discussing a kai ita da Nana, Kwata-kwata hankalinta ba ya kan Haajara da ta ƙi yin shiru ta ci gaba da maganar, Hankalinta a tashe yake a yanzu sabida jin abun da Nana take faɗa mata, Take zufa suka soma keto mata zuciyarta na tsananin buga wa sabida ruɗu da tashin hankalin halin da take ciki, Bata san ma an kawo gida ba sai da Haajara tayi mata magana, A firgice ta ɗago tana kallonta Ita kanta Haajara ta ga yanayin ta ya sauya gaba ɗaya ba a yanda ta zo ba, Shi yasa cikin damuwa take tambayarta, "Aunty Haseena mai kuma ya faru kika shiga wannan halin? Wani abun ne ke damun ki?" "Nothing." Ta amsa mata tana ƙoƙarin bude kofan ta fice. *** _____Haseena tayi ƙoƙarin ɓoye halin da take ciki sabida ganin Iyayenta, Sun yi murnan ganin ta but sauyawan nata yayi mugun basu mamaki suma, Har sai da suka kasa shiru suka hau ta da tambaya; musamman yanda ta taho har wani uwa duniya a haka da irin wannan shigan, Basu yi mata wani faɗa ba tunda dama ita ƴar gaban goshi ne, soyayyar da suke mata yasa ba sa ganin laifin ta, Kawai Abbansu ne yayi mata maganar shigan nata, yace, "kar ta ƙara zuwa a haka, nan da can ba ɗaya bane, ai yanzu kiwon mutane ake yi ba dabba ba, yanzu sai ya zama abun magana." Daga nan bayan sun gama gaisawa sai ta wuce ɗakin ta don yin wanka kasancewar a gajiye take, bare tana son keɓewa don ta samu mafita a kan maganganun da Nana ta faɗa mata, Ina gaskiya sam baza ta taɓa yarda da wannan sharaɗin ba, tun farko maiyasa ba a faɗa mata ba sai yanzu za a ce mata ana buƙatar wani daga cikin dangin ta, to wa zata bayar wa ƙungiya? Gaskiya bazai yiwu ba, hankalinta ya tashi ne da Nana tace mata, "a cikin Iyayenta dole ta zaɓi ɗaya ta sadaukar wa da ƙungiya, tunda haka ake yi sai kana bada jini, bazai yiwu kai kana shan jinin wasu ana biya maka bukatunka da na wasu ba; but kai baza ka bayar ba." Daƙyar tayi wanka ta sauya kaya ta koma Falo, kasancewar Umma ta dame ta ta fito ta ci abinci, hankalinta ba a jikinta yake ba don ta ƙosa ta samu damar da zata kira Nana suyi magana ta tsakani da Allah, domin bata yarda da wannan hukuncin ba, zata iya bada kowaye ne a cikin dangi ban da Iyayenta, Da wannan tunanin ta ɗan saki jikinta after ta ci abinci sun ɗan yi hira, sai tace, "zata je ta kwanta ta huta." Tana koma wa ɗaki ta kira Nana video call, Cikin damuwar da ya bayyana a kan face ɗin ta tace, "Nana, please understand me, Ni dai bazan iya bayar da Iyayena ba, ke ne kika saka ni a cikin ku ba tare da amincewa na ba, and yanzu kuma sai ku ce dole sai na bada iyayena a kan me? I can't gaskiya, but you choose kowaye nayi alkawarin zan baku ban da my parents." "Wani killer smile Nana ta saki before tace, "kin san mutanen da muka sadaukar a kan cikan burin mu ne baby? Dukkanmu babu wanda bamu bayar da ƴan uwa da Abokanmu ba, wannan shi ne sharaɗin kungiyar, kuma idan har kina so ki ci gaba da kasancewa cikin farin ciki to dole sai kin bi abun da aka ce miki, just iyayenki za ki bayar fa, ko ba ki bada su ba zasu mutu wata rana, think babyna yanzu da dayanzu ba ɗaya bane a cikin rayuwarki, i know yanzu kin gane abun da nake nufi da ke, ke kanki baza ki so ki rasa komai ba a yanzu." Sai tayi dariya ta ƙara da faɗin, "baby ko ba ki amince ba dole za ki rasa ɗaya daga cikin su, gwara tun wuri before time ya ƙure ki yanke hukunci, after parents you can give everyone in your family wanda ku ka fito ciki ɗaya." Gabanta ne ya faɗi sabida jin abun da tace, kenan zata iya sadaukar da ƴar uwanta Haajara? No ina bazai yiwu ba! Dukkan su tana son su baza ta iya ba, shiyasa kamar zata yi kuka tace, "Honey wlh bazan iya ba, su ɗin duniyata ne, ina matuƙar sonsu, bazan iya sadaukar da iyayena da kuma ƴar uwata guda ɗaya ba, na shaƙu dasu, su ne komai nawa, tun farko ba Ni na kawo kaina harkan ba, ke kika saka ni, meyasa baza ki taimake Ni ki cire Ni ba? domin bazan taɓa bada jinin iyayena a sha ba, No I can't bazan iya ba wlh, zan iya bada kowa ban da su, meye jin daɗin to babu su a raye?" Dariya Nana tayi tace, "Ni yanzu i have something to do, Ni dai na faɗa miki ki yanke shawara ɗaya before mu je meeting, domin a cikin su dole za ki bada ɗaya, idan kuma ba haka ba ke za ki mutu baby, Ni kuma bazan bari ki mutu ba." Sai tayi wannan shu'umin murmushin nata mai fassara da dama, take ta kashe kiran bata jira cewar Haseena ba Wadda tabar ta cikin zullumi da tashin hankali, tunda ta ambaci meeting shiyasa ta ƙi yarda ta kwanta sabida ta san cewa da zaran ta kwanta dole zata ganta a can, domin sau da yawa hakan ke faruwa da ita sai dai komai ya faru da ita kamar a mafarki ta ganta a cikin su, bata taɓa takawa ta je da ƙafafunta inda suke ba, sai dai idan ta kwanta barci tayi mafarki, kuma har ga Allah a wannan lokacin bata da kwanciyar hankalin da zata yarda tayi wannan barcin, bazai yiwu ta bada iyayenta ba, Wannan abun ne yasa gaba ɗaya Haseena ta shiga cikin wani hali da sam walwala ya ƙaurace mata Su kansu su Umma sun fahimci halin da take ciki, amma koda suka tambaye ta sai tace musu, "kawai gajiya ne, ba ta jin daɗin jikinta." Umma tace, "ta je ta kwanta mana tunda kwanciya tace zata yi but ta fito." Amma ta nuna sam a'a, a wurin ta kwanta saman dogon kujera sabida kar barci ya ɗauke ta, tana ta saƙe-saƙe a cikin ranta don samun mafita, ita dai ta jefa kanta ga halaka, at most of the time tana yin dana-sanin zuwan ta karatun nan, wani lokacin kuma sai hankalinta ya gushe musamman da ta soma jin daɗin rayuwarta tare da sauyin da ta samu a tattare da ita, takan rasa mai ke damunta wani time ɗin, idan zata yi tunani mai kyau sai kuma zuciyarta ta ƙeƙashe tunaninta ya sauya gaba ɗaya, bata san meyasa ba, amma a yanzu tana dana-sani don wlh baza ta taɓa bada iyayenta ba ko mai zai faru, tayi alƙawari duk wanda suke so a faɗin duniyar nan zata iya mallaka musu amma banda iyayenta da ƴar uwanta ɗaya tilo Tana nan kwance kiran SHAREEF ya shigo wayanta, Amma tsaban damuwa yayi mata yawa ta kasa ɗauka sai ma saka ta a silent tayi, yayi ta kira bata san ma yana yi ba sai da Haajara ta kawo mata nata wayan, ta faɗa mata, "SHAREEF ne ya kira yana nemanta." Bata ce komai ba ta amshi wayan ta wuce ɗakinta. [03/04, 10:48 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE12* _____Tun before ta shiga ɗakin nata ta amsa call ɗin, sannan ta shiga ta zauna a saman bed ɗin ta tana yin shiru da sauraron abun da yake furta wa Daga can other side SHAREEF kamar zai yi kuka yace, "Sweetheart What's going on? I called you and you did not pick up the phone, or there is a problem?" Sai da ta lumshe idanu ta buɗe, tana daidaita yanayin ta before tace, "No dear, kawai ina kwance ne sabida gajiyar hanya, kuma wayan tana silent ne that's the reason." "Hmm har kin sa na ji sanyi a raina, so ya kike? I hope komai normal ko? Na so ina kusa da sai in saukar miki da gajiyar, I didn't get to come, ina fata ba ki yi fushi ba?" Murmushin gefen baki tayi tare da kwanciya a saman gadon, a cikin jan hankali ta ba shi amsa, "No ban yi fushi ba, ai ba na fushi da kai dear, ka wuce wannan a wurina, i don't care da zuwan ka bcus na san zaka zo ne." "Yauwa sweetheart Thank you for believing me, I will come after Isha prayer, sai ki tanada min abu mai daɗi da tsarabana." Yayi maganar cikin kashe murya cike da ƙaunarta a rai in ten minutes they talked on the phone and ended up in love, Bayan sun gama sai Haseena ta kwanta a nan bata fita ba duk da ba barci take yi ba. Amma kuma ta kasa tashi sabida mugun nauyin da jikinta yayi mata; tamkar ana danne ta, tun ba ta jin barcin har wani nannauyan barci ya zo ya sure ta batare da ta shirya ba, Sai tsintan kanta tayi cikin ƙungiyar su tana gurfane gaban Ogansu da ke zaune a saman dogon kujerar sa, While sauran member suna tsaye sun yi musu ƙawa sun zagaye su sanye da jajayen kaya, Daga ciki har da su Nana sun yi cirko-cirko suna kallon Haseena da ke faman zare ido Ogan su da ke cike da fushi yake kallon wurin da Haseena take, cikin tsawa da amon murya yake furta maganar da turanci, "saƙon ki ya iso gare mu, sai dai kina gab da ki amshi mummunar hukunci in har kika nuna bijirewa a tare damu, don haka ki yi gaggawar yanke hukunci yanzu domin bamu da lokacin ɓata lokaci, wa kika zaɓa a cikin su?" Gaba ɗaya jikin Haseena rawa yake yi sabida kiɗime wa da tashin hankali, jikinta na rawa sai dai girgiza kanta take yi domin har a lokacin ba ta jin zata iya bada wani nata a kashe mata shi, never baza ta iya ba Kece wa yayi da dariya yana kaɗa sandan hannunsa, "kina ɓata mana lokaci Haseena, ba wai zamu tsaya muna sauraron ki bane a nan, idan kika yi mana gardama zamu halakar da ke yanzun nan, sai dai kina da zaɓi da dama na wani lokaci, ki yi gaggawar sanar mana da wanda kika zaɓa, domin kuwa muna buƙatar shan jinin sa a yanzu." Jin Haseena ta ƙi yin magana har yanzu, sai faman girgiza kanta take yi tana kuka tana son magana but ta gaza, Tuni Nana ta isa wurin ta tana duƙa wa a gabanta tare da faɗin, "please Haseena choose one, ba ki da lokaci da za ki ɓata mana time, akwai buƙatar a sha jinin nan yanzu if not; za ki fuskanci gagarumar matsala, kuma ba na son in rasa ki. Look Haseena." Ta kamo hannunta cikin lallami tana sake cewa, "Please ki zaɓi ɗaya shikenan fa. Hurry up, please don't waste time, you will slowly forget everything, baza ki yi maraichi ba, ki duba daulan da kike ciki Haseena, you need to be happy, everything will pass tamkar ba a yi ba." Daƙyar Haseena ta iya buɗe baki ta zaɓi ɗaya, shima sai da ta ga Ogan nasu ya fusata an soma juya ta za a gana mata azaba, shiyasa bata da zaɓi face miƙa wuya, kawai sai ta miƙa ƴar uwanta Haajara Nan take Ogan ya fashe da dariya, sai ga wani hayaƙi ya soma fitowa ta cikin bakin sa, muryansa mai fita bibbiyu ya ba Nana umarnin ta miƙa mata sweet ɗin da zata ba Haajara ta sha a yau din nan, ta tabbatar tayi aikin nan kafin mintina goma su cika Daga nan Haseena ta farka a gigice ta haɗa zufa kashirɓan kamar wacce aka tsamo ta a cikin ruwa, babu inda jikinta ba ya rawa tsaban kiɗima da zallan tashin hankali, Tana duba hannunta ta ga sweet ɗin ajiye, Wani irin kuka ne ya kufce mata tana furta, "Na shiga uku Ni Haseena, me nake yi haka? Wacce ƙaddara ce ta sa na shigo duniyar nan? Wlh bazan yarda ba, bazan iya ci gaba da kasancewa cikin mutanen nan ba, bazan iya ba, duk yanda za a yi sai na fita, ƴar uwata baza ta mutu ba, babu wanda zai mutu a cikin su." Kuka kawai take yi tana sambatu kamar zata shiɗe, Bata san cewa kukan nata yana fita da sauti sosai ba Da haka Haajara ta jiyo ta lokacin da ta hauro saman zata amshi wayanta, A nan ta taho a guje sabida jin sautin kukan ta, hankali a tashe ta ƙarisa wurin ta tana kiran sunan ta, "Aunty Haseena lafiya? Me ke faruwa da ke ne? Don Allah ki faɗa min wa ya taɓa ki; me aka yi miki?" Sai lokacin Haseena ta dawo cikin hayyacinta har lokacin jikinta bai dena rawa ba, ga gumin da ke ƙara tsatstsafo mata; face ɗin ta gaba daya ta nuna tashin hankali da tsananin ruɗin da take ciki, ta kasa ma magana don bata san me zata ce ba, illa kallonta da take yi zuciyarta na bugawa kamar zata faso ƙirjinta tuna tashin hankalin da ke gabanta, taya ma za a ce zata bada jinin ƙanwarta da ita kaɗai ce ƴar uwanta? Meyasa tayi wannan gangancin? No baza ta iya ba sai dai ko meye ya faru wlh Girgiza ta Haajara tayi tana sake faɗin, "wai lafiya Aunty ina magana kin yi shiru? Me aka faɗa miki kike kuka?" Saurin saka hannayenta tayi tana share hawayen ta, sai da ta share before ta girgiza mata kanta tace, "No babu..." "Babu kamar ya? Haba Aunty Haseena kina cikin wani hali mana, kuka fa kike yi kuma ki ce min babu komai? Don Allah ki faɗa min hankalina a tashe yake." "Nace miki babu komai Haajara, ki sarara min kin ji ko?" Tayi maganar cikin tsawa wadda bata san ma tayi ba sabida halin da take ciki Shiru Haajara tayi tana kallonta da mamaki, amma ta gaza magana cus tsawan da tayi mata, sai ta miƙe da sauri domin ta je ta sanar da su Umma, don ba ta ganin alamun akwai lafiya a tattare da Haseena a yanda dai ta ganta a haka Kamar Haseena ta san me ke ranta tayi saurin kiran sunan ta, "ban ce ki sanar da kowa halin da kika ganni a ciki ba, if not wlh zan yi mummunar saɓa miki Haajara." Tsayawa Haajara tayi tana kama ƙugu after ta juyo da kallonta gare ta, sai tace, "to me yasa baza ki faɗa min halin da kike ciki ba? Kina wannan halin sannan kike tunanin zan yi shiru bazan sanar da su Umma ba? Kuka fa kike yi Aunty Haseena, ko SHAREEF ne ya faɗa miki wani abin?" Sosai Haseena tayi ƙarfin halin danne zuciyarta, tare da ƙoƙarin daidaita kanta before ta furta, "yeah, it's me and SHAREEF, ba na son ki sanar dasu wani abu please Haajara, ki bar zancen nan a nan." Sai ta miƙe tana ajiye sweet ɗin da ta ƙanƙame a hannunta, tare da ƙoƙarin zame rigan jikinta don ba ƙaramin azaban zafi bane yake huro mata, ji take yi kamar an saka ta a wuta ana dafa ta, Shiyasa tuni ta zare rigan ta ajiye ta koma daga ita sai bra da pencil skirt, sai ta koma ta zauna yaraf har lokacin jikinta bai bar rawa ba Ita kuma Haajara mamaki ne sosai a kan face ɗin ta, mamakin Haseenan, musamman yadda ta ga tana fitar da hucin gumi alhalin babu zafi a garin, kuma ga AC a ɗakin but ita zufa ke keto mata, kuma ga alamunta ya nuna babu natsuwa ko kaɗan a tare da ita, sai dafe kanta take yi ta rasa inda zata saka ranta ta ji daɗi, Zuwa tayi gefen ta ta zauna tana kallon sweet ɗin da ta ajiye, but sai ta mayar da hankalinta a kan Haseenan tana cewa, "wai Aunty me yayi miki ne haka kika tayar da hankalin ki? Me ya faɗa miki? Ko dai wani auren ya ƙara?" Domin a hasashen ta babu abun da zai ɗaga mata hankali sama da wannan Amma sai Haseena ta watsa mata wani mugun kallo tana mai ɗaure fuska tamau, "i said leave me alone Haajara, wai uban me kike so ki ji ne? Kin takura min fa." Saurin ɗaga mata hannu tayi tace, "yi haƙuri Aunty Haseena don Allah maida wuƙan, sorry ba Ni nakar zomon ba.., Allah na damu ne da halin da kika shiga, idan ba ni yar uwanki ba; wa kike dashi da za ki faɗa mishi damuwar ki? Ki yi hakuri don Allah." Sai kuma ta mayar da idanunta a kan sweet ɗin tare da ɗauka tana ƙoƙarin buɗe wa, Har ta buɗe da ninyar sakawa a baki domin Haseena bata kallonta, Before ta saka a bakin ne take cewa, "Aunty wannan mintin fa; mai ban sha'awa...?" Tun kafin ta ƙarisa maganar Haseena ta ɗago tana kallonta, a firgice ta wafce mintin cikin tsananin tsoro idanunta tuni sun firfito waje kamar zasu faɗo ƙasa Ita kanta Haajara ta tsorata da yanda Haseenan ta wafto mata hannu har tana bige ta, abun ya ɗaure mata kai, sai kawai ta saki baki tana kallonta galala kamar wata sabuwar halitta While ita kuma tuni ta sakar mata wani kallo a zuciye tace, "fita, just leave my room now." Zata yi magana ta daka mata tsawa, "fita don ubanki tun kafin in falla miki mari." A yadda ta ga ta hayayyaƙo mata dole ta tashi ta fita tana taɓe baki, tare da ƙunƙunai tana faɗin, "a kan wannan mintin don jaraba shine kike min wannan uban tsawan? Aikin banza." Ta ja dogon tsaki ta fice tana bugo ƙofan Haseena ta ji ta sarai amma bata kula ta ba, tana fita itama ta miƙe tana safa da marwa cikin tsananin tashin hankali da tunanin mafita, Zuwa tayi ta ɓoye mintin a cikin kayanta sannan ta dawo ta zauna tana dafe kanta, wasi-wasi take yi a ranta anya baza ta aikata abun da suka ce ba? No, ba ta jin zata iya, amma mene ne mafita? Idanunta sun kaɗa sun yi jazur gaba ɗaya ta sake fita a hayyacinta, "Ni dai Nana kin kaini kin baro, nayi dana-sanin sanin ki a rayuwa, ko don sabida soyayyar dangina dole zan fita a wannan harkan, bazai yiwu ba, daga yau bazan sake komawa ba na dawo kenan." Ta furta maganar a fili tana mai fashewa da wani kuka mai cin rai, "wai mai ya hau jikina ne?" Sai ta zamo ƙasa ta haɗa kai da gwiwa tana ci gaba da kukan mai tsuma rai. *** _____Inda ita kuma Haajara Falo ta koma ta tarar da Umma zaune ita kaɗai Umma tace, "ina Haseenan ne? Ko tayi barcin ne?" "No, tana nan a ɗaki, ita ta koro Ni ma, yanzu haka SHAREEF ne ya ɓata mata rai ta nemi ta juye a kaina." "Ya ɓata mata rai kuma? Ba na jin haka sai dai in ke ce kika tone ta." Tura baki Haajara tayi tana cewa, "kai Umma! komai dai laifina kike gani, kin san Aunty Haseena da saurin ɗaukan zafi, abu kaɗan ma sai ta hau min faɗa, amma ban yi mata komai ba wlh, zuwa nayi na ganta cikin damuwa but na tambaye ta sai ta juye fushin a kaina." Hararanta Umma tayi tace, "ke ma fa da shegen neman tsiwa ne, kin cika shishshigin tsiya shiyasa faɗa ke haɗa ku da ita, common tashi ki ɗauko min fruits ɗin da na ajiye a kichen, yana nan a freezer ki dauko ki yanka ma Abbanku before ya fita yanzu." Miƙe wa Haajaran tayi, sai dai tuni ta ɓata fuskarta tana cewa, "komai dai Ni ce mara gaskiya Umma, Shikenan daga yau bazan sake shiga harkan ta ba Insha Allahu, dukka-dukka yaushe ne zata tafi ma tabar mana gidan namu." Ta wuce tana ci gaba da ƙunƙunan maganar ta Ita kuma Umma kaɗa kanta kawai tayi bata ce komai ba tana mayar da hankali kan kallonta Shiga kichen ɗin tayi tana ɗan waƙe-waƙen ta har da taka rawa kamar yadda ya zame mata jiki, sai rausayawa take yi a haka ta karisa jikin freezer ɗin ta buɗe, Bayan ta ɗauko faffaɗan bowl din sai ta wuce inda suke ajiye wuƙa da nufin ɗauka, A nan saman kanta ta ga sweet sak irin wanda Haseena ta hana ta, abun ya bata mamaki don sanin Haseena bata shigo kichen ba balle ta ajiye irin sweet ɗin, Sai kuma tayi dariya tace, "an hana Ni sha sai ga shi na samu tsuntsu daga sama gasashshe." Tuni ta ɗauki mintin ta ɓare ta jefa a baki tunda sha'awa ya bata, ga shi ƙato da alamun zai yi dad'i ne since ta tabbatar dole Haseena ta zo dashi, ba irin sweet ɗin nan bane Har ta ɗauki wuƙan zata fice, amma me; sai ta ji maƙogwaron ta ya soma riƙewa wani irin zafi ya ziyarce ta, da sauri ta ajiye bowl din tana kama wuyanta sabida azaba kamar an sa mata wuta, tuni ta jefar da sauran mintin while cikin ta yayi wani irin murɗa wa, Kafin ƙiftawan ido jikinta ya rikice da wani irin azaba wanda tuni ta soma fita a cikin hayyacinta, ganin jini na zuba ta hancinta nan da nan ta ƙwalla ƙara tana kiran sunan Umman su, Ko kafin Umma ta taho tuni ta zube a wurin jikinta ya saki babu sauran motsi; sai jinin da ke ɓulɓulowa ta hanci da bakin ta kamar an kunna famfo, Ragowar mintin kuma ya ɓace ɓat babu shi a wurin. [04/04, 12:12 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE13* _____A ganin Haseena har sai ta ba Haajara mintin nan sannan zasu iya kashe ta, bata san cewa ba haka bane, iya lokacin da suka ba Mutum to dole sai sun aiwatar da ƙudirin su a kansa, bare su suna da tsafi mai ƙarfi, ganin zata yi musu taurin kai shiyasa suka ajiye mintin da kansu don Haajara ta gani, kuma ta ɗauka ta sha kamar yanda suke buƙata Haseena na cikin daki ta soma jin kukan Umma tana kiran sunan Abbansu, Daga ita har Abban suka fito a gigice sabida jin kiran da babu lafiya a cikin ta Lokacin Umma ihu kawai take yi tana faɗin, "Haajara... Haajara." Hannunta na rawa tana nuna hanyar kichen Gaba ɗayansu ta faɗar musu da gaba, musamman ma Haseena da zuciyarta ke faman buga wa tana tsaye babu riga a jikinta sabida tashin hankali, bata tsaya sauraron abun da Umma take faɗa ba sai ta sauka da gudu ta nufi hanyar da take nuna musu, Ko kafin takai ta jiyo Umman su tana faɗin, "Haajara tana kichen ba ta motsi, jini na zuban mata..." Ai da gudu ta sha kwanan kichen ɗin tana ruga wa a guje ta shige ciki, tana ganin Haajara a zube ga jini na kwance a saman tayes ɗin, take ta daddaro idanu waje tana rufe bakin ta cikin tsaninanin kiɗima A lokacin shima Abba ya taho a guje; Umma na mara masa baya, Gaba ɗayansu suka nufe ta suna kwaɗa mata kira zuciyarsu kamar zata buga don tashin hankali Umma sai kuka take yi tana girgiza ta, "Alhaji wlh bata motsi. innalillahi..! Ta mutu, Alhaji mu taimaka mata mu kaita asibiti jini na zuban mata." Maganar take yi cikin fitan hayyaci tana girgiza Haajaran Shi kansa Abba yanda jikinsa ke rawa kamar mazari ya kasa ɗaukan ta ma, Sai Umma da ta tallabo mishi ita suka ɗaga ta zasu fitar da ita Haseena na tsaye kamar gunki har suka fitar da ita, da sauri ta taka ta fita ta bi bayansu tana sakin wani uban ihu mai ƙara, yanda ta fita hayyacinta sam ta manta a yanda take babu riga sai bra Su kansu su Umma basu ankare da ita ba har suka shigar da Haajaran cikin motan, Ma'aikatan gidan duk sun taho wurin hankali a tashe sabida jin ihun Jama'ar gidan, ga yanda aka taho da Haajara na ta zuban jini har yanzu ta bakin ta da hancin ta Ganin sun shige gaba ɗaya zasu tafi, ga Haseena a haka babu ɗankwali bare riga; babu mai takalma cikin su, sai sharɓan kuka take yi Ɗaya daga cikin mai aikin su tayi saurin cewa, "Ma'am, babu riga a jikinki fa, bari in dauko miki rigan." Tafada da sauri tana juyawa da gudu ta koma cikin gidan Su kansu sai lokacin suka kula da ita, Umma tace, "ta sauka kar ta ɓata musu lokaci." Amma furr Haseena ta ƙi fita tana ta kuka ta haɗa gumi domin ita kaɗai ta san abun da ke damun ta, tabbas tana da tabbacin ƙungiyar su ne suka shanye wa Haajara jini tunda ta ga halin da take ciki Sai da suka jira mai aikin ta kawo mata doguwar riga before Abba ya ja suka fita, direct sai asibiti Abun da basu sani ba, ko kafin su isa rai yayi halin sa, Koda Likitoci suka amshe ta sun shiga sun duba ta but sun gane babu rai a jikinta, har gwaje-gwaje sun yi domin gane abun da yasa take blending amma basu gano komai ba, Dole yasa suka fito suka sanar da Iyayenta, Take Umma da Haseena suka yanke jiki suka faɗi, sai dai aka ɗauke su zuwa dakin emergency don duba halin da suke ciki. ***** _____After Isha prayer kamar yanda SHAREEF yace ma Haseena zai zo, yana dawowa sallah bai tsaya cin abinci ba ya je yayi wanka ya kimtsa ya dauki wanka cikin ƙananan kaya da suka yi masa kyau, sai tashin ƙamshi yake yi zuciyarsa farin ƙal da farin cikin ganin abar ƙaunarsa, Har ya gama yana ɗaura agogo a hand right din sa, Sai ga Hanif ya shigo ɗakin yana waya, Ɗago kai yayi ya dube sa sabida jin yana ambaton sunan Mahmud, Fahimtar abun da suke tattaunawa a kai ne yasa ya mayar da hankalinsa kacokan a kansa, har ya gama ɗaura agogon before ya dawo wurin sa ya tsaya; hannayensa zube a aljihun wandon sa ya tsira masa ido yana kallonsa Sai da Hanif ɗin ya gama wayan before ya dube sa shima yace, "Finally Mahmud ya gama aikin sa, domin yanzu haka ya samo inda za a ga Mutumin, yanzu ya rage aikin mu sai mu san ya za a yi." Hannu ya tafa ya furta, "Wow!" Face ɗin sa ɗauke da murmushi wanda har dimples ɗin sa sun bayyana, Cike da farin cikin jin zancen yace, "very good. I enjoyed this talks Hanif, yanzu ka kira Mahmud ya san yanda za a yi ya samo mutanen da zasu kama mana shi, and ya san inda zai ajiye mana shi zuwa gobe mu fara aikin mu. Now I don't have time, idan na dawo zamu ci gaba da magana." Ya ƙare maganar da duba wrist watch din sa Hanif yace, "but you didn't tell me where you are going?" "Zan je wurin sweetheart ne yau ta dawo." "Oh! Haka, I forgot Haajara ta sanar min fa." Sai ya taɓe baki yana miƙe wa da faɗin, "to sai ka dawo, a kula da kai." Kallonsa SHAREEF yayi, sai dai bai ce komai ba ya juya ya ɗauki wayansa da ke saman dressing mirror, Suka fita a tare but shi ya bi ta benen da zai sada shi da ƙofan baya ya fice a gidan, While Hanif kuma ya wuce Falo After ya isa gidan, a bakin gate yayi packing tare da yin horn, sai kuma ya bude murfin motan yana sako da ƙafarsa ɗaya waje, yayinda ya ɗauki phone din sa ya soma latsawa yana nemo numban Haseena, kira yayi tana ring but ba a yi peaking ba, almost 3times yana kira before ya dakata, ya ɗaura hannunsa a sitiyarin motan ya ƙara danna horn da ƙarfi har sau biyu A time ɗin ne Mai gadi ya leƙo domin ya ga wane ne, don a tunanin shi masu gidan ne suka dawo, sai dai saɓanin haka; motan SHAREEF ya gani a fake, Da sauri ya fito ya nufi wurin sa yana duƙa wa har ƙasa ya soma gaishe shi A daƙile SHAREEF ya amsa ba tare da ya kalle sa ba, wanda a lokacin ya ƙara kiran numban Haseenan ne ko zai samu, Sai ya tsinkayi muryan Mai gadi yana faɗa masa abun da ke faruwa, Da sauri ya juya yana kallonsa, hankalin sa ya ɗan tashi ko da jin yanayin yanda yake tambayar mai gadin, "tun yaushe hakan ta faru?" "Sun yi awa ɗaya da tafiya Alhaji." Bai tsaya sauraron sa ba ya shigar da ƙafarsa tare da ɓame murfin motan, ya tayar da sauri yayi gaba ya je yayi reverse before ya wuce da gudu, although ya san asibitin da suke zuwa that's why ya wuce can kansa tsaye Ko lokacin da ya je ƴan uwan su Abba har sun cika asibitin don sun san me ke faruwa, Lokacin Umma ta farfaɗo suna koke-koke Haseena ce ke can ɗaki har time ɗin bata farka ba, Tana can cikin ƙungiyarsu hankalinta a tashe da ta tabbatar da cewa jinin ƙanwarta aka sha, Sai dai basu bata damar yin magana ba sabida yanda Ogansu ya fusata da ita, Sai dai yayi mata uzuri ne sabida ganin har yanzu bata cika ƙai'dojin ƙungiya ba, sabida sau tari hakan na faruwa wasu tsoro yana saka wa su fita ko su yi ƙoƙarin tona musu asiri, sai dai da zaran sun fara shayar da shi jinin ɗan uwansa to sun gama da wannan babin, wannan shi ne babban sirrin su da suke ƙara kangarewa idanunsu ya buɗe tsoro ya fita a ransu, Dalilin da yasa bayan sun gama tsafe-tsafen su; Haseena aka fara ba jinin ta shanye shi dolen ta, Tun daga nan kuma kanta ya soma juyawa ɓacin ran da ke tare da ita ya soma gushe wa, take ta manta da wani tunanin jinin ƴar uwanta da aka sha, zuciyarta ta ƙeƙashe tana jin komai zata iya yi don jin daɗin ƙungiyar su, bata da wata matsala yanzu, Ko daga yadda ta bada haɗin kai suka gudanar da meeting tuni sun san sun gama da ita, don haka sun san baza ta sake basu wata matsala ba Sai da suka gama meeting din sannan ta farka a cikin wani yanayi, idanunta sun kaɗa sun yi jazur kamar jini ya taru a cikin su SHAREEF yana ɗakin da aka kwantar da ita, don tunda ya san halin da take ciki hankalinsa ya fi na kowa tashi, A lokacin ma tuni an wuce da gawan Haajara; sai shi SHAREEF ɗin da ya zauna wurin Haseena yana jiran ta farka, Yana ganin ta buɗe ido ya riƙo hannunta yana kiran sunanta, Amma ganin yanda idanunta suka canza launi hankalinsa yayi mugun tashi; cus a tunanin sa duk sabida rashin ƴar uwanta ne ta shiga wannan halin Ita kuma a wannan lokacin babu wani raɗaɗin rasa ƴar uwanta, don haka ta miƙe zaune tana kallon ɗakin da take, before ta sake kallonsa tace, "dear, me nake yi a nan ne?" Hannunta ya kama cikin kwantar da murya yace, "tun ɗazu kika fita hayyacinki ba ki farka ba sai yanzu, hankalina ya tashi sosai I thought I'd lose you, please sweetheart ki ɗauki ƙaddara kinji? Mutuwa na kan kowa; kowa zai mutu, Allah ya bamu hakuri da juriya." Shiru tayi tana ɗan tunani, sai kuma tace, "ina su Umma?" "Sun tafi gida gaba ɗaya yanzu, bari in kira likita sai ya duba ki ina zuwa." Ya furta hakan yana sakin ta before ya juya in quickly ya fice Tana nan zaune bata motsa ba sabida yanayin da take ji babu daɗi a jikinta, sai faman lumshe idanu take yi kamar wata wacce ta sha maganin barci, idanunta a hankali suka soma washe wa tun buɗe idanun da tayi Likita na zuwa ya duba ta yana tambayar inda ke mata ciwo a halin yanzu? Sai ta nuna, "babu komai, gida zata wuce." Ganin haka ne yasa Likitan ya sallame su suka fita waje tare da SHAREEF, a motan sa suka wuce zuwa gidan su, Wanda tuni ya cika maƙil da jama'a duk da dare ne, Kuma a halin yanzu an bar gawan sai zuwa gobe za a yi jana'izar ta, Sai koke-koke ake yi gunun ban tausayi Yayinda Haseena kuwa ko hawaye basu ƙara fita a cikin idanunta ba, babu wanda ma yake gane halin da take ciki tunda dare ne, tana zaune ne kawai cikin ƴan uwa tayi shiru ba ta cewa komai. *** _____Zuwa washe gari aka yi jana'izar Haajara aka kaita makwancin ta, wadda mutuwar ba ƙaramin girgiza ahalin ta yayi ba in ka cire Haseena a cikin su, tabbas mutuwar farat ɗaya abun kokawa ne, bare kuma budurwa ƙaramar yarinya like her Haka aka ci gaba da karɓan gaisuwa koyaushe su SHAREEF suna zuwa gidan, Dalilin da yasa ma basu bi takan mutanen da Mahmud ya tabbatar musu a halin yanzu suna hannu bA Ƙarshe dai Hanif ne ya je wurin su shi da Mahmud suka tuhume su a kan laifin da suke tuhumar su dashi, Da farko basu samu abun da suke so ba sai da suka gana musu azaba sannan suka faɗa musu gaskiya, Hanif yayi musu video a lokacin da suke maganar, sannan ya tura ma SHAREEF Sai da SHAREEF ya gani ya duba ya tabbatar sun samu abun da suke so, sannan yace, "su miƙa su wurin ƴan sanda su shigar da ƙara, shima yana nan zuwa before su wuce." Bai bar wurin ba sai da ya samu ganin Haseena domin ya ga halin da take ciki, don ya damu da ita sosai, tun ranan sau ɗaya suka sake haɗuwa; ga shi har yau kwana uku kenan, ko wayanta ba ya samu ko ya kira ba ta ɗauka, dalilin da yasa yake damuwa kenan duk da yana mata uzuri sabida halin da take ciki, Amma koda ya ganta yau ya ji daɗi sosai don bai zaci zai ganta ta washe sosai ba, kamar ba ita ba, har farin cikin sa ya yalwata yana ta jin daɗi Dayake akwai mutane a falon Abban nasu, bai ja lokaci ba yayi mata sallama ya wuce, a cewar sa; "zuwa gobe zai sake dawowa." Daga nan station ya wuce a can ya tarar da su Hanif, lokacin sun gama shigar da ƙaran suna tattaunawa da DPO, SHAREEF yace, "ba ya son a ɗauki lokaci mai tsawo don suna da hujja a hannunsu, a gaggauta danƙo su Alh. Inuwa a miƙa su kotu, a can zasu biya abin da suka yi." A ranan kuwa aka je har gida aka taho da Honourable Ja'e, don shi kaɗai aka samu a gida, Alh. Inuwa ba ya nan yana Abuja, Don haka suka tura masa saƙon dawowarsa nan kusa sabida ƙaran da aka shigar a kansu Duk da hankalin su ya tashi da jin wanda ya shigar da su ƙara, but basu wani ɗaga hankali sosai ba, sabida sun san babu ta yanda za a yi su bari SHAREEF ya ci galaba a kansu, suna da hanyar da zasu bi wajen ganin bai samu nasara ba, Ko kusa basu yi tunanin an kama mutanen da suka saka aiki ba, don haka a washe gari Alh. Inuwa ya dawo garin, A ranan kuma aka je aka taho da Shuraihu da wasu mutane biyu da suka yi ɓarnan; masu aiki a Companin SHAREEF, tunda sunan su duk ya fito a bayanan mutanen da aka kama, Nan fa ido ya raina fata don basu taɓa tunanin har haka SHAREEF ya samu hujja ba, Sai dai a cikin su babu wanda ya amsa gaskiya sun ƙaryata bayanan da mutanen suka faɗa Inda aka shigar da maganar kotu zuwa gobe za a yi zama kamar yanda SHAREEF ya buƙata Duk wannan abun Dady bai da labari sai da Hanif ya sanar mishi da komai a yau, Yayi mamaki da al'ajabin maganar, kuma hankalin sa ya tashi matuƙa da ya ji dalilin da yasa suka yi asarar kayan, Sai yace ma Hanif, "ya kira SHAREEF yanzu ya zo ya same shi." After ya zo Dady yace, "wai dama abun da ke faruwa kenan SHAREEF baka taɓa faɗa min ba? Why?" Shiru SHAREEF yayi bai ce komai ba "Kenan ta sanadiyyar samun gwangilan nan ne har suka ƙona mana kaya muka yi asara? Meyasa tun farko ka dauki abun nan da zafi tunda har sun nuna suna son hannun jari a ciki; why baka basu ba?" "Dady, ba Ni na hana su hannun jari ba, already mu aka siyarwa daga baya suka shigo cikin maganar, and Ni a ganina kowa yana bukatar ci gabansa; don me zan ɗauki ɗaukakan mu in ba wasu after all bamu rasa kuɗin da zamu iya siyan hannun jarin ba? Mutanen nan suna adawa da mu ne ba sa son ci gabanmu, duk inda suka ga zamu ƙaru sai sun shigo ciki, don me zan bar su ina gani suna son komar da mu baya bazan ɗauki mataki ba?" Girgiza kansa Dady yayi duk da ransa ya ɓaci sosai, sai yace, "amma SHAREEF ba a yin haka a Kasuwanci, ka kasance mai haƙuri da so wa ɗan uwanka abun da kake so wa kanka, idan da ace tun farko ka ɗauki wani abu daga ciki ka basu; da duk hakan bata faru ba, hakan bazai rage ka da komai ba SHAREEF, shi yaƙi ɗan Zambo ne; haka kasuwanci ɗan haƙuri ne, akwai faɗuwa akwai samu, ka ga sabida haka ga abun da suka aikata mana, nan gaba bamu san mai zai faru ba, a hakan da kake ganin ba komai ba sai ka riƙa tara maƙiya; daga ƙarshe su kaika su baro, Ni yanzu ban san ma me zance ba sabida abun yayi muni da yawa, tun farko da na sani zan ce mubar su da Allah ne kawai, duk abun da Mutum yayi ya yi wa kansa ne, ka dena cewa sai ka rama komene ne aka yi maka, ka zama mai yafiya SHAREEF, don Allah ka sauya wannan halin naka ba na son kana ɗaukan zafi a kan irin wannan matsalolin na rayuwa; wanda mun san cewa babu wanda ya fi ƙarfin Allah ya jarrabe shi, babu wanda yake wuce ƙaddaransa, Kai kuma har da kai ka biye masa Hanif; ina ganin ka da ɗan sauƙin kai, ban ji dadi ba wlh, kar ku sake yin abu makamancin irin wannan kuyi shiru baku sanar min ba, waɗannan mutanen manyan mutane ne, yanzu idanun duniya zasu dawo kanmu, ba na so kun ji ko?" Gaba ɗayan su gyaɗa kansu suka yi; duk da shi SHAREEF bai ji daɗin yanda Dady ya ƙi goya musu baya ba, a ganin sa ai haƙƙin su ne, idan ba a koya ma ire-iren waɗannan mutanen hankali su shiga taitayin su ba; to nan gaba abun da zasu yi sai ya fi haka, yanda suka shuka tsiyan su dole su girba, ba su zasu yi asara ba; su da suka assasa gobaran su zasu girbi abun da suka shuka, kawai su biya su shine kwanciyar hankali Dady shi kuma nasiha ya dinga musu sabida shi har ga Allah bai ga amfanin abun da su SHAREEF suka yi ba, ai duk wanda ya cuce ka shi da Allah ne, ba ga shi ba duk da asaran da suka yi basu faɗi ƙasa ba, Allah na buɗo musu ta hanyoyi da dama, ba wancan dukiyar shi ne kaɗai abun da suke dashi ba, tunda daɗin abun akwai inda zasu biya wata rana, kowa bazai shuka mugunta sannan yace hakan ya tafi a banza ba, dole zai girbe sa ko a gaban Allah; ko wani iftila'in ya faɗo musu.*** A washe gari aka yi zaman kotu aka gabatar da tuhumar da ake musu, sun so musawa amma ganin videon nan, da kuma koro jawaban da mutanen nan suka sake yi, hakan yasa dole su Honourable Ja'e suka amsa laifin su, kuma suka faɗi dalilin da yasa suka yi haka Babu ɓata lokaci Alƙali ya yanke musu hukunci kamar yanda suka saka su asarar duk kayan da suka rasa, zasu biya su a nan take babu jingirta wa, Sannan da kuma taran da aka ci su sabida gobaran da suka assasa haka kawai, idan da a ce Allah bai tsayar da abun a haka ba; da ba a san halin da ake ciki ba a yanzu, maybe ma har a rasa ran wasu mutanen, Don haka ba ɓata lokaci aka basu damar su biya shi Cikin baƙin ciki da takaici haka su Honourable Ja'e suka biya maƙudan kuɗaɗen nan da basu dashi a wannan lokacin, Tunda sun bayyana basu da halin biya Yayinda SHAREEF ya miƙe ya basu damar, "zasu iya siyar da hannun jarin su, shi kuma zai siya babu ɓata lokaci, in sun amince yanzu a yi ciniki." Haka kuwa aka yi, komai ya tafin ma SHAREEF yanda yake so, sai jin daɗi yake yi yau ya samu abun da yake so, ya ci galaba a kan maƙiyansa, mai ya fi wannan daɗi? A kullum farin cikin kasancewar sa mai Nasara, idan har zai yi nasara a kan maƙiya ya ga baƙin cikin su, hakan ya fi masa komai daɗi, ga shi kuwa yau ya saka su sun yi nadamar abun da suka yi, musamman yanda idon mutane yake kansu duk wani mai ganin su da mutunci; manyan mutane da alhazzai suna ganin abun da ke faruwa, Yaro Karami ya gama da su, ya ci musu mutunci ya tozarta su a bainar duniya, wanda basu taɓa tunanin hakan ba, tabbas SHAREEF ya shammace su. [06/04, 12:16 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE14* _____Tun sati ɗaya da rasuwar Haajara; Haseena ta so ta tafi, sabida tamkar a ƙaya take jin ta, baza ta iya dogon kwanaki babu Nana a tare da ita ba, baza ta iya zama a nan babu ita ba sabida tsananin kewa da buƙatar ta, domin ita kanta Nanan kullum sai ta dame ta a kan ta dawo, Har cewa tayi ma, "in har bata dawo ba zata biyo ta nan." Amma sai Haseena ta dakatar da ita tace mata, "zata dawo nan kusa ta bata lokaci." Bata sanar da iyayenta zata tafi ba a washe gari bayan kwana bakwai, sai da ta haɗa kayanta sannan ta sanar musu zata wuce, bayan tayi musu karyan, "ana neman su da gaggawa ne a kan karatun su." Duk da haka sai da Umma tace, "bazai yiwu ta tafi ba sabida mutuwa ce aka yi, kuma ai bata yi yawan hutun ta ba, dukka-dukka kwanaki takwas da zuwan ta, ta bari ko arba'in in an yi sai ta wuce. " Haseena tace, "No Umma bazai yiwu in ƙara kwanaki a nan ba gaskiya, sabida zan iya samun matsala gwara kawai in wuce." Umma zata sake magana; amma Abba ya hana ta, yace, "kawai ta barta tunda harkan karatu ne, tafiyarta bazai sa Haajara ta dawo ba, gwara ta tafi kar ta samu matsala kamar yadda ta faɗa." Daga nan suka yi mata fatan alkhairi har bakin mota suka raka ta, driver ya wuce da ita zuwa airport After Haseena tayi landing a Sydney, Sai daga baya ta sanar da SHAREEF domin bai san da tafiyarta ba, sai da ya kira ta sannan take sanar mishi, "ita yanzu haka ta wuce." Tsaban takaici da mamaki ma ya rasa mai zai ce mata, yanzu ya soma fahimtar Haseena ta rage sonshi, ko ya yarda ko kar ya yarda tabbas Haseena ta canza mishi, matsayin da ta ba shi a baya; yanzu ba haka ba, tunda har zata tafi bata sanar mishi ba sai yanzu da ta isa can, ya ma rasa mai zai ce mata tunda bai da bakin magana, amma yayi mamaki gaskiya tunda mutuwar ƙanwarta aka yi; bai yi tunanin zata tafi nan kusa ba, kuma a yanzu din ma bai tambayi ba'asi ba haka ya kashe wayan yana takaicin ta, ga shi babu halin ya nuna mata ɓacin ransa sabida yanda yake jin tsananin soyayyarta a zuciya, a yanzu ji yake yi tamkar ya rabu da ita, yana son Allah ya cire masa wannan soyayyar da bata da amfani a wurin sa, da zai sami hakan tabbas da yayi farin ciki a ransa A ranan haka ya wuni sukuku ko abinci ya kasa saka wa a cikinsa, damuwa ce fal cikinsa ya rasa inda zai tsoma kansa ya ji daɗi, meyasa komai ya canza; yanda yake zato ba haka ba? Why Haseena zata sauya mishi maimakon ta ba shi farin ciki take wahalar dashi? A kullum soyayyarta ƙara ninkuwa yake yi a ransa, koda da ƙwaran zarra na wucewar daƙiƙu ba ya wucewa batare da tunanin ta ba Dalilin da yasa lokaci ƙanƙani rayuwarsa ta sake canza wa, domin a yanzu ba shi da wadataccen farin ciki tunda Haseena ba ta ba shi kulawa yanda yake buƙata, abun da yake so a wurin ta ta hana sa, wayan ma da yake samu suna yi sai idan ita ta ga damar a yi sannan za a yi, Idan ya ɗauki ƙafa ya je can bazai samu farin ciki ba, sai dai kawai yana zuwa ne domin ya samu salama daga cikin zuciyarsa, tunda ganin ta ma wani samun natsuwa ne a tattare da shi, walwalan sa yanzu ta ragu fiye da baya, duk da daman shi ba mutum bane mai sakin fuska, amma yanzu damuwa ta ƙara mishi yawa, Idan ya zauna bai da aiki sai tunani a ransa, ko ɗan wayan da zaka gansa ya zauna yana latsawa ba ya yi yanzu, tunda wacce suke charting ɗin yanzu ta janye mishi, Lokaci guda ya zabge duk ya wani sukurkuce tamkar ba ɗan gayen nan ba mai ban sha'awa da kyan kallo, yanzu babu wannnan gayun tunda babu natsuwar yin sa, kallo ɗaya ma idan ka yi masa zaka san cewa ya sauya duk ya fita a hayyacinsa, ya rame ga ciwo da koyaushe fama yake yi da kansa Hanif ne mai rarrashinsa tunda shi ne ya fi sanin halin da yake ciki, Yakan ba shi shawarwari da dama musamman a kan Maryamu, amma sam ba ya kula sa bare ya nuna alamun yana jin sa, A koyaushe yana nuna masa kan cewa, "shi ya ɗaura ma kansa wannan laluran tunda yana da damar da zai iya magance matsalar sa, Haseena a yanzu bata da lokacin sa sabida ko yanayin da take nuna masa dole zai fuskanci hakan, yakamata ya san me yake yi kafin ya halakar da kansa." Cike da sanyin murya SHAREEF yace, "na sani Bro, na san Haseena ta sauya daga ra'ayina yanzu, amma abun takaicin yanda zuciyata ta makance da tsananin ƙaunarta, a duk sakon ɗaya ina jin soyayyarta tana ƙara ninkuwa fiye da koyaushe, da zan samu na fitar da sonta a zuciya tabbas zan so hakan, Hanif ina cikin tashin hankali, ita kaɗai nake so, ba na jin zan iya kallon wata Mace a fuskata ta bani sha'awa bayan ita, bazan iya kallon wata bayan ita ba, amma ina mata uzuri na san komai zai wuce da zaran ta kammala karatunta ta tare a gidana, haka nan zan jure tunda bazan iya aikata zina ba." Cike da tsananin tausayinsa Hanif ya dafa sa yana kallonsa, yayinda yake furta, "ina ji a jikina Haseena baza ta sauya ba, sabida a yanzu rayuwarta ta sauya ba kamar baya ba, kuma na tabbata a can inda take ta koyo wasu dabi'u wanda duk mai hankali zai iya fahimtar hakan, wlh sam yarinyar bata dace da kai ba Bro, ni na tabbata alhakin yarinyar nan zai iya kama ka, kamar yanda kake jin zafi da ƙunci a ranka, haka itama Maryam tayi fama da dakon soyayyarka tana azabtuwa, amma sam ka ƙi tausaya mata, meye laifin yarinyar; meye aibun ta? Don kawai Allah ya yi ta a cikin ƙauye ba irin rayuwar wayewan da kake so ba? Ka sani yanda ka wahalar da ita; kaima haka zaka ɗanɗani irin wannan azabar, ko ba don ka so ta ba; ka sassauta mata daga irin tsanar da kake mata, watakil Allah zai sassauta maka kaima a naka soyayyar, imagine! Ka taɓa tunanin Haseena zata juya maka baya bare har ta baka wannan wahalar?" Sai ya girgiza kansa tare da ci gaba da faɗin, "shawaran da zan baka kawai yanzu ka dage da addu'a domin samun sauƙin wannan makauniyar soyayyar naka da baza ta kaika ko'ina ba, already yanzu Haseena idanunta sun buɗe fiye da na da, illan wayayyun Matan kenan; don su basu da alƙibla a koyaushe zasu iya juya maka baya su nuna sun fi ƙarfin ka, ɗan samun lokacin ta da kake yi ma yanzu zaka iya rasawa a nan gaba, sabida ta canza daga wacce ka santa." Shiru yayi bayan yakai zancen sa nan Yayinda ɗakin ya ɗauki shiru babu wanda ya sake yin magana tsawon lokaci, sai ma SHAREEF ɗin da ya miƙe ya nufi cikin bedroom ɗin su daga shi sai short wando, yana tafiya tamkar zai faɗi ƙasa tsaban yanda yake jin yanayin sa babu daɗi While Hanif ya bi sa da kallo har ya shige, sannan ya girgiza kansa yana mamakin halin ɗan uwan nasa, ya san bazai taɓa ɗaukar maganarsa ba kasancewar sa mai tsaurin ra'ayi, Murmushi kawai yayi ya tashi ya fita a cikin Falon Yayinda SHAREEF kuma yana shiga; toilet ya wuce kansa tsaye, domin rabon sa da yayi wanka tun jiya, ko fita yau bai yi ba sabida ciwon kan da ya dame sa, a nan ɗaki ya wuni sai dai Sadiq ne ya kawo masa abincin sa har nan, kuma ko taɓa wa bai yi ba sai yanzu da Hanif ya dawo, shi ya tilasta masa har ya ɗan ci kaɗan suka zauna suna tattaunawa a kan matsalar nasa, Wankan yayi ya fito ya zura riga da wando masu sauƙin nauyi na shan iska, ko lotion bai tsaya ya shafa ba don yanzu bai ɓata lokacin sa a kan ƙalƙale kansa; sabida halin damuwa da yake ciki, duk ya bar gashi a face ɗin sa yayi buzu-buzu ya sauya mishi kamanni, tamkar ba shi ba, madaidaitan idanun nan sun sake shige wa sun yi ciki sun faɗa, duk wanda ya kalle sa sai ya ga ramar da ke face ɗin sa, Room slippers ya zura a kyawawan fararen ƙafafunsa before ya fita zuwa downstairs Su Hanif suna zaune a falon suna taɓa hira, ban da Dady ba ya cikin gidan a lokacin Zuwa yayi ya zauna a gefen Hanif yana ɗan kwantar da kansa a jikin kujerar Yayinda Momy ta bi sa da kallo tana faɗin, "ka ji sauƙin kan yanzu?" Kai ya gyaɗa mata bayan da ya ɗago yana kallonta Sai tayi shiru tana kallonsa before ta kiran sunan sa da faɗin, "har yanzu SHAREEF baza ka yi wa kanka faɗa ka san abun da ya dace da kai ba ko? Meyasa ba ka jin magana ne? Ka fi son ciwo ya kashe ka a banza wato? Kana ganin ba na shiga lamuranka a tunanin ka abun ba ya damuna ne? Kana fama da ciwo tsawon lokaci, mun yi maka gata amma ka kasa bin ra'ayin mu, ita wacce kake so bata yi maka maganin komai ba, Don Allah ji be yanda ka rame ka fita a hayyacinka sabida taurin kai irin naka, ka saka mu cikin damuwa kai kanka baka da natsuwa ko kaɗan, idan har zaɓin mu bai yi maka ba mun yi kuskure, zai kyautu a ce ka nemo wata Macen ka aura tunda Allah ya halarta muku zama da Mace fiye da ɗaya, ba wai ka zauna kana cutar da kanka kullum kana ɗaga mana hankali ba, wlh ka ji na rantse maka idan har baka samu mafita tsakanin ita wacce kake so da Maryam ba; idan har babu wacce zata zauna da kai to dole ka ƙara aure, don bazai yiwu muna ji muna gani ka faɗa halaka ba, daga ƙarshe ka zo kana aikata zina; na faɗa maka ka ɗauki mataki tun kafin mu mu ɗauka." Shiru yayi ya sunkuyar da kansa ya kasa cewa komai, to mai zai ce? bai da bakin magana, yanzu Haseena ta sare mishi gwiwa, abun da take mishi yana matuƙar ƙona mishi rai, bai taɓa tunanin zata ci amanarsa ko ta nuna mishi halin ko-in-kula irin wannan ba, abun baƙin cikin kuma ba ya son kowa sai ita, ba ya jin zai iya zama da wata Mace bayan ita, bare wancan yarinyar da ya tsana, tun farko bata yi masa bane, hasali ma ba shi da ra'ayin Mace baƙa irin ta, ga kuma abubuwan da tayi masa, a ganin sa sam bata da kamun kai tunda har zata iya nuna soyayyarta a gare shi bayan ba shi yace yana sonta ba, bata yi masa ba sam, zai iya zama da kowacce Mace ban da ita, Shiru yayi kawai yana sauraron Momy wacce ta dage sai faɗa take mishi amma bai ce uffan ba, don yanzu magana ma wannan wahala take mishi, halin da yake ciki ya ishe shi, Bai ce mata uffan ba har ta gama suka sauya hiran su ita da Hanif, yana zaune tamkar wanda yake sauraron su amma hankalin sa kacokan ba ya wurin su, ya mayar da kansa ya kwantar idanunsa a buɗe ya tsira wa sama ido yana faman tunani Sadiq kuma na gefe saman one sitter yana ta faman latse-latsen laptop, shima hankalinsa ba ya gare su, ta aikin gabansa kawai yake yi Sai da aka kira magriba sannan suka tashi gaba ɗayansu suka ɗaura alwala suka wuce Masjid Sai bayan magriba shima Dady ya dawo gidan, Bayan sun je sun yi sallan isha'i suka zauna hira but ban da SHAREEF kamar koyaushe, shi ya soma zuwa ya ci abincin sa sannan yayi musu sai da safe ya wuce ɗakin su While su kuma suka zauna hira sai kusan ƙarfe tara before su hau kan Dinnig su ci abinci, A lokacin ne ma Momy take sanar musu da zuwan Maryamu sati mai zuwa idan sun samu Hutu, zasu zo gaba ɗaya har da su Ammee. *** *** *** _____Bayan su Maryamu sun samu Hutun su, gaba ɗaya suka tarkato sai ga su sun dira a Kano da ƙarfe biyu na ranan Alhamis. [08/04, 5:20 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE15* _____A ranan SHAREEF bai je ko'ina ba, tunda yanzu bai cika zuwa aiki ba sai jifa-jifa sabida yanayin jikinsa, don a yanzu bai cika lafiya ba, Yana kwance a ɗakin sa yana sharan barci, duk bidirin nan da aka yi na zuwan su Ammee bai da labari, Lokacin har su Aunty Zainab sun zo sun tafi ma bai sani ba, Yana kwance sai kusan ƙarfe huɗu sannan ya tashi, Jiki a mace ya miƙe ya wuce cikin toilet, wanka ya soma yi before ya ɗaura alwala, ya fito ya shirya kansa cikin baƙin wando da jan t.shirt wadda ta ɗan sakin masa bata kama sa ba; kuma tana da kauri da dogon hannu, wurin mirror ya nufa ya tsira wa kansa ido yana kallon yanda ya koma, yanda ka san wanda yayi jinyar watanni haka ya koma, don ma gashin da ke face ɗin sa ya rufe masa ainihin raman da yayi, sajen sa ya fito sosai yayi tsawo, haka ma gemun sa kamar wani Balaraben Ustaz haka ya koma, fuskarsa tayi jazur haka laɓɓansa sun yi jazur kamar wanda ya shafa janbaki tsaban ja, yayinda idanunsa suka shige sosai suka ɗan tasa sai haske da suka ƙara tarwai da su, gashin kansa ya bi da kallo yana faman shafa gefen kumatun sa da hannunsa ɗaya, gaban gashin kansa yayi tsayi sosai kamar wanda za a ƙitsa, ƙeyansa kuma babu komai sai ɗan gashi kaɗan da ya toho, Ɗan numfashi ya ja yana mai lumshe idanunsa before ya buɗe yana sake kallon kansa, shiru yayi na tsawon lokaci yayinda yake faman kitsa hanyar da zai bi don magance matsalar sa, har yanzu ba ya samun sukuni daga azabtuwar da yake yi na soyayyar Haseena, komai ya ƙi ya sauya, yau rabon su da suyi waya kwana uku kenan, yana matuƙar kewarta da kewar jin muryanta, Ɗan juya wa yayi yana kallon wayansa da ke ajiye a saman gado, yayi shiru yana tunanin ya ɗauka ya kira ta ne ko a'a? sabida ya daukar wa kansa Alkawarin in har ba ita ta kira sa ba bazai sake kiran ta ba, cuz ko ya kira ƙarshe ɓata mishi rai zata yi ta ƙi basa lokacin ta, dole sai ita ta kira don kanta sannanne zai iya samun time ɗin ta, Janye idanunsa yayi yana nufan wurin takalmansa ya zura slippers green colour; sannan ya fice a dakin ba tare da ya dauki wayan ba, A hankali yake taka matattaƙalan benen yana sauka, idanunsa ne suka faɗa a kan bayanta; wanda bai samu ganin fuskarta ba sakamakon juyawan da tayi riƙe da plates a hannu zata kai kitchen, Tsayawa yayi cak yana kallon bayanta sabida ba ƙaramin tafiya dashi tayi ba, yanda mazaunan ta suke juya wa cikin baƙin siririn skirt ɗin da ta sanya ya tsuke ta, ya fitar mata da ainihin shape ɗin ta mai ban sha'awa da ɗaukar hankali Sanye take da milk color din riga wanda aka yi sa da lace, an yi design mai shoki na gefe ɗaya, rigan bata da tsayi iya ƙugunta ta tsaya, sai dai shokin da aka yi ne na gefe ya sauka har wurin gwiwarta, sai siririn baƙin skirt ɗin da ke jikinta, Kanta kuma sanye da hulan turban; wanda aka yi da lace ɗin rigan Yanda bayanta ya ja hankalinsa ya kasa ɗauke ido a kanta har ta shige cikin kitchen ɗin, a ransa kuma yana mamakin wace ce wannan mai irin wannan sura mai ban sha'awa? har bayanta ya ɗauke masa hankali ina ga ta juya gabanta, ji yayi har cikin ransa yana bukatar tozali da ita domin ƙare wa wannan kyakkyawan jikin nata kallo, Ya kasa ci gaba da tafiya yana tsaye a tsakiyar benen, yayinda ya ɗaura idanunsa yana zagaye ilahirin falon da kallo babu kowa sai sauran plates da aka ajiye a tsakar falon While Maryamu koda ta ajiye plates ɗin a kitchen, sai ta juya da nufin kwaso sauran, Dayake plates ɗin da suka ci abinci ne har da waɗanda su Aunty Zainab suka ci suka tafi, while su Momy sun shiga yin Sallah, Ganin ita kaɗai ta rage tunda ba ta sallah shiyasa ta fito ta soma kwashe kayan da nufin ta wanke before su Aakifa su fito, Koda ta fito falon bata kula da SHAREEF da ke tsaye a kan bene ba, hankalinta yayi gaba wajen kwaso sauran plates ɗin Inda a nan take idanuwansa suka yi masa tozali da wacce yake kallo, har ga Allah a farko bai gane ta ba tunda bazai iya tantance kamannin Maryamu ba, cuz a baya ba kallonta yake yi ba sabida yanda ya tsane ta, bare yanzu da tayi fresh duhun skin dinta ya ragu sosai, ta koma kamar irin dack Choco colour din nan mai ban sha'awa da ɗaukar ido, Idanun nan nata sun ƙara tarwai dasu masu zubin ƙwai girmansu ya ƙara fitowa sosai, musamman da ta saka tozali, Tayi light makeup a fuskarta wadda yayi tsari da zubi na fuskarta; ya kuma ɓoye mata kamannin ta Tun daga sama har ƙasa yake kallonta, ba komai ya fi daukar hankalinsa ba irin kyakkyawar surar jikinta da yayi matukar fizgar tunaninsa ya sanya shi a wani irin yanayin da ya kasa fassara shi, har wani haɗiye miyau yake yi tsaban yanda surar jikinta ke rawa a idanunsa, tabbas Allah yayi halitta a wurin nan, Yanda ka san maye haka yake bin ta da kallo har sanda ta sake shigewa kitchen ya kasa ɗauke ido a kanta, Sai da ya ji motsi a gefe guda sannan ne ya mayar da hankalinsa a kan Aakifah da ta fito daga ɗakin Maryamu Itama irin shiganta sak da na Maryamun, domin su uku aka yi musu ɗinkin, Tana kokarin wuce wa kitchen ne ta hange sa a wurin, shiyasa da murnanta ta kira sunan sa tana washe masa baki Sai lokacin ya gane ita ce, amma yayi mamakin ganinta tunda bai san da zuwan nasu ba, in fact ma bai da labari, A hankali ya soma takowa zuwa ƙasan yana bin ta da kallo har ya sauka While ita kuma tace, "Yaya SHAREEF, tun ɗazu muka zo muna ta neman ka aka ce kana barci, ina wuni?" "Lafiya, ke da wa ku ka zo?" Cike da murna tace, "mu da su Ammee ne, sun shiga yin Sallah basu fito ba. Bari in kira maka su Yusaira suna ɗaki suma." Guntun murmushi yayi yace, "no bar su, bari in je in yi sallah zamu gaisa in na dawo." Yayi maganar yana wuce wa batare da ya jira amsar ta ba, sai dai har yakai bakin ƙofa yana kallon hanyar kitchen ɗin ko zai ganta ta fito, sabida har lokacin bai fahimci wace ce ba, amma ganin Aakifah sai yake tunanin ko dai Yusaira ce? Amma bai yarda a ransa ita bace tunda ita tana da haske ba kamar wannan da ya gani ba, duk da haka yana zaton maybe wata bakuwar ce, har ga Allah bai taɓa tunanin Maryamu bace tunda bai taɓa kawowa a ransa zata iya koma wa kamar wannan ba, in fact ma da tsawo da jiki duk wannan ta fi Maryamun da ya sani, kuma bazai iya tantance ta ba tunda ba ya kallonta, bai da lokacin ta ma balle ya santa Sallan yayi ya dawo, a lokacin su Ammee sun fito falo suna zaune Aakifah da Maryamu kuma suna kitchen suna wanke-wanke Da gudu Na'ilah ta ƙarisa wurin sa tana faɗin, "oyoyo Yaya Hanif. Sannu da zuwa." Kama ta yayi yana ɗan murmushi sabida jin sunan da ta kira sa dashi, domin har yanzu ita bata bambance su sabida kamannin su, in har ba ta gansu wuri ɗaya bane, kuma dama can ba wani sanin su tayi ba, Ɗaukar ta yayi daƙyar; ya taho inda su Ammee suke zaune, Zama yayi a kan sofa before ya kira sunan Ammeen fuskarsa a sake Ta amsa shi tana murmusawa da faɗin, "kana can kana ta barcin ka abun ka, Aunty tace baka da lafiya ne?" Amsa mata yayi before ya gaishe ta Ta amsa tana tambayarsa jikin nasa? "Na ji sauƙi Aunty." Yusaira itama gaishe shi tayi, Ya amsa ta a takaice yana kallonta Ammee tace, "ga shi nan duk ka rame SHAREEF, gaba ɗaya ka sauya kamanni, Ni farko ma ban gane ka ba wlh; ka zama ustazun ƙarfi da ya ji wato?" Ta ƙare da ƴar dariyan ta Momy kuwa taɓe baki tayi tace, "kema dai kin faɗa, ya ɗaura ma kansa abun da ya fi ƙarfin sa, kullum a kwance yake yana fama da kansa." Kallonsa Ammee tayi tace, "SHAREEF wai yaushe ne ita yarinyar zata gama karatun ne?" Shiru yayi, sai kuma yace, "i don't know Aunty." "Kana nufin baka sani ba?" Tayi maganar da mamaki Gyaɗa kansa yayi batare da ya kalle su ba, idanunsa a kan Na'ilah da ya ɗaura a jikinsa tana jan masa gemu, Ba wai bai sani bane; bai son su ja zancen ne tunda ba ya son maganar "Hmm lallai! To Allah ya kyauta." Momy tace, "Amin dai, dama kin dena biye masa a kan abun haushin nan, don Ni kwata-kwata ba na son a yi maganar yarinyar, yayi ta zama a haka har Mahadi ya bayyana, akwai ma maganar da zamu yi; bari Dadyn su ya fito sai mu zauna muyi magana." Daga haka suka ci gaba da hiran su a tsakanin su, While Yusaira tuni ta mike ta wuce kitchen wurin su Maryamu Yayinda SHAREEF yana zaune a wurin yana ɗan wasa da Na'ilah, jefi-jefi yana biye mata a kan surutun da take mishi, Har zuciyarsa kuma tunanin yarinyar da ya gani ɗazu yake yi; don ta tsaya mishi a rai Lokacin kuwa sai ga Maryamu ta fito tana yarfe hannayenta, Kamar an ce ya ɗago kai suka haɗa ido da ita, Tsira mata ido yayi, while itama hakan ne wacce ta kafe sa da nata manyan idanun suna kallon-kallo a tsakanin su, Kamar shuɗewar seconni biyar tuni ita tayi saurin janye nata idanun tana mayar wa a kan su Ammee, Yayinda ta tako a hankali ta nufo wurin kanta tsaye cikin takun ta mai fizgar hankali SHAREEF kuwa ya kasa dauke ido a kanta duk da yana tunanin kamar gizau take mishi, gani yake yi kamar ita kamar ba ita ba, sai da ya ji Momy ta ambaci sunan ta before ya gasgata abun da zuciyarsa ke hasasowa, Take ya sake ware madaidaitan idanunsa a kanta A lokacin itama ta sake kallon inda yake, karaf suka haɗa ido dashi, wani kallo ta watsa mishi kafin ta janye nata idanun luuu kamar zata yi fari cikin wani irin yanayi mai ɗaukar hankali Wanda sai da ya ji gabansa ya faɗi; jikinsa yayi wani irin yamm har sai da yayi zillo kamar zai tashi tsaye; sabida yanda ya ji wani irin abu ya tsikare sa tun daga tafin ƙafansa zuwa ƙwaƙwalwan sa, take ya lumshe idanunsa yana sake bude wa a kanta, sai dai tuni ya ɗauke idanun ya sake rufe su sabida son gasgata abun da idanunsa suke son nuna masa, Shiru yayi yana sauraron Ammee wacce take magana yanzu "Maryam ɗauko min wayata a ɗakin Aunty, na baro ta a cikin Jakana kar a kira ni." "Ok." Tayi maganar tana yin gaba zuwa steps Ɗago kai SHAREEF yayi direct ya bi bayanta da kallo, wanda bai san lokacin da zuciya ta rinjaye shi ya mayar da ido a kanta ba, cus surar jikinta ba ƙaramin mugun fizgarsa tayi ba, wanda hakan yasa ya kasa danne abun da yake ji ya ɗaga kai yana faman bin ta da ido; cike da mamakin sauya mishi da tayi fiye da tunanin sa Daga Momy har Ammee duban SHAREEF suke yi, domin dukkansu suna son su ga halin da zai nuna idan ya ganta, tabbas ba ƙaramin mamaki suka sha ba da suka ga yanda ya kafe ta da idanu ko ɗauke su ya ƙi, Sai da suka kalli juna cike da mamaki suka sake mayar da idanunsu a kansa, Basu yi masa magana ba har sanda suka ga yana shirin jiyowa a sa'ilin da Maryamun ta ɓacewa ganin sa, Da sauri suka dauke ganin su a kansa suna kama wani zancen Shi kuwa tuni ya lumshe idanunsa yana jin yanda zuciyarsa ke luguden bugawa, Wai anya yarinyar da ya raina ne ta zama haka a ɗan ƙanƙanin lokaci; ko kuma wata ce? Zuciyarsa ta kasa yarda da cewan ita ce don ba ƙaramin mugun sauya mishi tayi ba a ido, abun da bai sani ba rashin kallonta da bai yi ne a baya yasa yake ganin kamar an sauya ta, shi a baya baƙar fuskar kawai yake iya hangowa da kuma ƙauyancin nata, amma lokaci guda ga ta ta zama santaleliyar budurwa abun sha'awa, uwa uba yanda ta haɗa ƙira mai matukar fizgar sa, domin ba ƙaramin yanayi ya shiga ba tsaban yanda yake ganin tana tafiya komai nata na rawa, har ji yake yi kamar ciwon sa zai tashi, Take a nan ya miƙe zumbur yana sauke Na'ilah a kan jikinsa, ya nufi hanyar steps ɗin da nufin bin bayanta, don a yanda yake ji bazai iya dakatar da kansa da kwadayin tozali da ita ba Baki sake suka bi sa da kallo, don babu wanda yayi yunƙurin tsayar dashi, Sai da suka ga ya haye saman before suka bushe da dariya, domin ba ƙaramin mamaki halin da SHAREEF ya shiga ya basu ba, tun yanzu ji be yanda ya koma daga ganin Maryamu "Wai Aunty kin ga abun da nake gani kuwa? tun ba a je ko'ina ba mutumin namu yana son afkawa, ko dai gizau abun ke min? Ban zaci haka ba wlh." Momy dariya tayi tace, "lallai namiji bai da ta ido, tun ba a je ko'ina ba kenan ya fara bamu mamaki, ai ban taɓa tunanin zamu iya ganin sauyi a nan kusa ba, ki ce komai zai zo mana a sauƙi kenan." "Wlh Aunty na ji daɗi sosai da na ga wannan yanayin da ya nuna, alamun nasara kenan, bare ƴar namu tubarakallah Masha Allah! Na tabbata babu namijin da zai kalle ta bai faɗa tarkon ta ba, ba ƙaramin tausayinsa nake ji ba musanman yanda na ga ya rame ɗin nan, Allah yasa dai kar ya ci gaba da mana taurin kai, Ni a ganina in har ya nuna yana son zama da ita kawai ta tare; da mu rasa shi." Girgiza kai Momy tayi tace, "ai bazai ma yiwu ba, ko ya nuna yana so wlh sai Maryam ta gama karatun ta, babu gudu babu ja da baya, ya je can ya nemi wata ko ya je wurin ɗaya Matar tasa, Ni fa ba ƙaramin burge ni Maryam tayi ba da ita ta iya kame kanta a gaban shi, ban taɓa tunanin haka ba, lallai Maryam tayi hankali." Ganin su Yusaira sun fito daga kitchen; shiyasa suka sauya hiran nasu. *** _____Cikin zafin nama Maryamu ta ƙarisa saman ta shige cikin ɗakin Momy, sai da ta shiga ta rufe ƙofan before ta jingina bayanta da ƙofan tana sauke ajiyar zuciya, hannunta a saman ƙirjinta ta runtse idanunta, numfashi kawai take sauke wa kamar wacce tayi tseren gudu, Ganin sa ba ƙaramin famo mata da zuciya yayi ba, a tunaninta ta birne soyayyarsa na har abada, amma ganin sa, ganin sa sau ɗaya tak ya ruguza mata dukkan wani natsuwa nata, ba ƙaramin dauriya tayi ba wurin cije wa har ta iya kama kanta ta kasa mishi kallo na uku, har yanzu akwai soyayyarsa da ke matuƙar wahalar da ruhin ta, sai dai yanda ta ɗauki alkawarin baza ta taɓa nuna wa a fili ba, hakan yasa ta danne komai ta binne tunaninsa a ranta, amma koyaushe yana cikin zuciyarta, domin soyayyarsa tamkar wata rubutacciyar ƙaddara ce da babu yadda za a yi ta cire ta na har abada, A yau kallon fuskarsa tamkar ya famo mata gyambon ta ne, fuskarsa kawai take iya hango wa a cikin idanunta, Buɗe idanun tayi tana jan numfashi kamar zata shiɗe, ƙoƙarin daidaita kanta take yi amma yanda jikinta ke rawa gabanta na matuƙar buga wa; sam natsuwa ta gagare ta, ƙafafuwan ta sun yi mata nauyi wanda yasa ta kasa motsa wa a wurin, rufe idanunta ta sake yi yayinda fuskarsa ta ƙara bayyana a cikin ƙwayar idanunta, ba ƙaramin sauya mata yayi ba, kamar ba SHAREEF ɗin da ta sani ba, Tsawon mintina biyar tana a wurin ta kasa kataɓus, sai da tayi matukar jarumta before ta daidaita kanta ta nufi wurin Jakan Ammee ta dauki wayan, sai ta tsaya tana sauke numfarfashi a kai -a kai tare da furta, "calm down mana Maryamu, ki natsu don Allah, kin yi alkawarin baza ki taɓa bari ya gane akwai soyayyarshi a cikin zuciyarki ba, kin yi alkawarin za ki kama kanki ki zama Mace mai aji, yanzu ba Maryamun da ya sani bane da, ki kwantar da hankalin ki kin ji ko? Ki kama kanki ba na son shiririta." Tayi maganar a fili kamar tana maganar da wani, Sai kuma ta saki ƙayataccen murmushi tare da cije laɓɓanta, Direct ƙofa ta nufa zata fice A lokacin SHAREEF na tsaye a bakin ƙofan, tun hawan sa ya zo ya tsaya a wurin ya ƙi gaba ya ƙi baya, burin sa kawai ya sake sanya ta a ido, tunaninsa ma ba ya jikinsa bai san abun da yake shirin aikata wa ba, kawai dai umarnin zuciyarsa yake bi Tana buɗe ƙofan suka kusa cin karo don bata taɓa tunanin zata tarar da mutum a wurin ba, kawai fitowa tayi gadan-gadan amma sai tayi saurin jan burki kamar wacce ta ga abun tsoro ta zaro manyan idanuwanta waje tana kallonsa Shima zuba mata idanun yayi duk da yanda yake jin wani yanayi da yanda ta tsare sa da manyan idanuwan nan nata masu firgitar dashi, masu saka mishi faɗuwar gaba, ya kasa yin magana illa bin baby face ɗin ta da kallo da yake yi; wanda sai a yau ne zai iya cewa yayi mata kallon tsanaki Maryamu wacce itama natsuwarta ta soma guje mata, daƙyar ta iya dauriya sabida yanda take jin zuciyarta na beating kamar zata fito ƙirjinta, Ganin ya ƙi ɗauke ido a kanta ga shi kuma ya kare mata hanya, daƙyar ta daure bata kawar da nata idanun ba, ta ƙura masa ido ƙirr tare da tsuke fuska babu ko ɗigon walwala a face ɗin ta tace, "zan wuce." Saurin ƙifta idanunsa yayi, amma bai iya matsa wa a wurin ba sai dai ɗan kame-kame da yake yi gaba ɗaya ya daburce, domin sai yanzu yake dana-sanin tsayuwar sa a wurin, ko me ya kawo sa oho? "Na ce zan wuce Malam, ka matsa min a hanya ko in bi ta kanka." Tayi maganar a tsawace tana banka masa harara Take ya waro ido yana bin ta da kallo cikin tsananin mamaki, Ai kuwa bai yi aune ba ya ji ta bangaje shi ta wuce da saurin ta ko waige bata yi ba, Tsananin mamaki da takaicin abun da tayi masa ya kasa kataɓus a wurin, yayinda yake takaicin abun da ya aikata, A ransa yana tunanin anya yarinyar da ya sani ne a baya? Yarinyar da ya gama kuri a kanta amma ita ce yau ta kalli tsaban idanunsa take furta masa magana har da daka masa tsawa, yayi baƙin ciki da takaicin biye wa zuciyarsa har ta rinjaye shi ya biyo ta, ya manta wace ce sai yanzu da tunanin sa ya dawo jikinsa, Ya ɗauki tsawon lokaci a wurin yana jiyo hayaniyar su a ƙasan Falo har da Dady, sai kuma can jiki a sanyaye ya ja ƙafafunsa zuwa ɗaki don ya kasa koma wa Falon, Ɗaki ya shiga ya zauna yana harɗe ƙafafu tare da kwantar da kansa face ɗin sa yana kallon rufin dakin, shiru yayi yana sauraron yanda zuciyarsa take buga wa, ya rasa ma wanne irin tunani yakamata yayi, har a lokacin mamakin sauyawan Maryamu yake yi, musamman yanda ya ga girman ta a idanunsa, da zaran ya rufe ido kyakykyawar surar jikinta ne yake masa ƙawa, ƙwaƙwalwan sa ta hautsine da tunanin yanda aka yi ta koma haka, kamar wannan yarinyar da irin ƙirar jikin manyan mata, don gani yake yi ko Haseena bata da wannan cikan jikin, ko a yanzu da tayi ƙiba surar jikinta bai fizge sa kamar yanda ya ga na Maryamu ya ruɗar dashi ya saka shi a wani yanayi; yake jin matsananciyar sha'awarta ba, Amma kuma dole ya kama kansa don bazai so mutuncin sa ya zube ba, ko don kuri da cika bakin da ya gama yi a baya, kawai ya san sheɗan ne ke masa ƙawa da saka shi cikin tashin hankali, amma har yanzu kamar wannan yarinyar bata kai matsayin da zai zauna yana tunaninta ko ya ɓata lokaci a kanta ba, Don haka tuni ya soma latsa wayansa don ya cire komai a ransa Yana nan zaune sai ga Hanif ya shigo ɗakin, "Bro, kana nan ashe?" Ɗago kai yayi yana dubansa, face ɗin sa ba walwala ya amsa mishi a takaice Ajiye Jakarsa yayi yana zama fuskarsa ɗauke da murmushi, ya kalli SHAREEF ɗin yana cewa, "i know ka san da zuwan su Ammee?" Shiru yayi sai dai ya tsira mishi ido yana jiran abun da zai ce; don a tunaninsa wata maganar mai muhimmanci zai yi Shi kuwa Hanif murmushin sa da biyu yake yi don yanda ya ga Maryamu ta sauya, ba ƙaramin farin ciki yayi ba, musamman yanda SHAREEF ya raina ta sai ga shi a lokaci ƙanƙani ta sauya kamar ba ita ba, ta zama yar Gayu ta waye, ya san dole yanzu SHAREEF ya ƙyasa, don haka yace, "wai kuwa ka ga Maryam? amazing ta zama yanda kake so, ta tashi a ƴar ƙauyen da kake ganin ta." Ya ƙare maganar yana ƙyalƙyale dariya Ba ƙaramin shaƙa SHAREEF yayi ba, "and so what Hanif? Don ta zama haka shine kake tunanin zata burge Ni? Har yanzu bata da kwalitis ɗin da nake buƙatar Mace, har yanzu kallonta nake yi a ƴar kauye Bagidajiya, Haseena ta fi min ita sau dubu, ita ce zaɓina ba wannan ba, gwara ka dena wannan tunanin, idan na ce ba na so ba na so ne, bazan taɓa so ba." Ya ja tsaki yana mayar da kansa ya ci gaba da latsa wayansa, don ba ƙaramin haushi Hanif ya basa ba Shi kuwa dariya yayi don ya ƙara ƙular dashi yace, "ni fa sai yanzu na sake tabbatarwa Maryam da Haseena suna da bambanci, bama zaka haɗa su ba, don Maryam kalan Matan da ake so ne yanzu, kowanne namiji zai yi fatan ya same ta, But Bro ka bi wannan shawaran da zan baka." Shiru SHAREEF yayi masa don ba ƙaramin ƙulewa yayi da maganganun da yake faɗa masa ba, tsaban takaici ma ya kasa magana bare ya kalle sa While Hanif kuwa bai fasa faɗan abun da yayi ninya ba yace, "why not kawai ka rubuta mata sakin ta ka huta da wannan ƙiyayyar da kake mata? ka ga zuciyarka zata huta itama haka zata huta da tsangwamar ka." A fusace SHAREEF ya ɗago yana kallonsa, "da can kai ka aura min ita da zaka ce in sake ta? Ko kana tunanin bazan iya sakin nata bane kake min wannan banzan maganar Hanif?" Kafaɗa ya ɗage tare da taɓe baki yace, "No ba haka bane, amma to meye amfanin ɓata lokacin ana abu ɗaya? Don itama yarinyar ta samu wacce take so, amma yanzu da auren ka zaka tauye mata haƙƙinta ne, irin su rububi ake musu nan da nan zaka ga tayi wani auren." "Enough Hanif.." Sai kuma yayi shiru tsaban ɓacin rai, ya miƙe yana jan dogon tsaki yabar Falon ya shige bedroom ɗin su Shima miƙe wa yayi ya bi bayansa yana dariya a ransa; da tunanin abun da zai faru nan gaba in SHAREEF ya kamu da soyayyar Maryamu, tabbas zai so hakan, kuma a lokacin ne zai maimaita masa maganganun da yayi na cika bakin bazai so ta ba, yana fatan Allah ya nuna masa wannan ranan ko don yayi masa dariya. [09/04, 5:38 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE16* _____Kasancewar su Ammee sati ɗaya zasu yi su koma gaba ɗaya, zasu bar Maryamu ita kaɗai zata zauna ta ƙarisa hutun ta, shiyasa tun a washe gari suka soma ziyarar ƴan uwa, tunda Ammee tana daɗewa bata zo ba sakamakon aikin da take yi at anything tana busy, don haka zuwan nan ziyara kawai ta dinga yi, kuma duk inda zasu je tare da Maryamu suke zuwa Gidan Aunty Najwa suka soma zuwa a washe gari, suka yi wunin su a can. The following day suka wuce gidan Aunty Fatimah can Jigawa, duk da itama a nan Kano take zaune, daga baya ne aka yi wa Mijinta canjin wurin aiki ta koma can da zama, bata taɓa haihuwa ba, ita ce wacce Momy take bi, sai kuma Autan su wato Ammee ita ce ƙarama A ɗakin su Momy su shidda ne cif da mahaifiyar su ta haifa ta rasu, lokacin Ammee tana karatunta a nan BUK har an sanya mata ranan aure, a lokacin ne suka rasa mahaifiyarsu, ta tafi ta bar su cikin kewa da ƙulafucin ta Mahaifin su Mata huɗu yake dashi da Yaransa a ƙalla zasu kai su goma sha takwas, shima Allah yayi masa rasuwa daga baya lokacin Mahaifiyar su Momy ta mutu da kusan watanni tara Har da Momy aka tafi Jigawan, tare da su Sadiq, amma SHAREEF ya ƙi bin su, don shi ya nuna sam bazai je ba, babu wanda ya matsa mishi suka wuce gaba ɗaya har Hanif, sai dai su a ranan suka dawo shi da Sadiq suka bar su a can, Sai da suka kwana da yamma suka dawo Washe gari kuma suka je gidan Aunty Salma daga nan suka biya gidan Aunty Zainab, Haka suka dinga zagaya dangi a ɗan kwanakin nan da zasu yi, Wannan dalilin ne yasa sam Maryamu ba ta haɗuwa da SHAREEF, sabida ba sa wuni a gidan, da sassafe suke fita kuma sai dare ko gabanin magriba zasu dawo gidan, Sannan shi SHAREEF bai cika zama cikin su ba koda sun zo cin abincin dare ne, ya kan sa Sadiq ya kawo masa har ɗaki ya zauna a can ya ƙi fitowa, hakan kuma yana yi ne duk saboda hana idanunsa ganin Maryamu, ba ya ƙaunar tozali da ita don kar ya zubar da girmansa, domin yanda jikinta ke fizgar sa da son kallonta sam hakan na ƙara mishi takaici da haushi, musamman in tana mishi gizau a idanunsa, dalilin da yasa yake janye jikinsa ya kame girman sa gudun raini Yayinda Maryamu sam bata san ma yana yi ba, domin a wurin ta abun farin ciki ne ma saboda rashin ganinsa da bata yi, har cikin zuciyarta itama ba ta son tana ganin sa sabida yadda take jin tana diririce wa damuwarta ta dawo sabo; haka ma soyayyarsa. Tayi tunanin zata iya jurewa ta cire soyayyarsa a rai, musamman yadda ta ɗauki tsawon lokaci bata ganin sa, amma ashe ba haka ba, juriya kawai take yi wajen kawar da kanta a gare sa har tayi kamar bata san da shi ba a rayuwa, amma a ƙasan zuciyarta tsantsan ƙaunarsa da tsananin son ganin sa ne yake addabar ta, tamkar zuciyarta zata fashe don azabtuwar da take yi wurin jin ƙuna da tuƙuƙi kamar ana hura mata wutan ƙaunarsa, ji take yi kamar ta dinga kurma ihu idan ta keɓe wuri guda babu mai ganin ta, amma sam ta gagara yin haka, sabida alkawarin da ta ɗaukar wa kanta a kan baza ta sake zubar da hawaye a kansa ba, hakan ne yasa abubuwan suka yi mata yawa a kullum jin ƙirjinta take yi kamar ana mata suya, wani abu ya dunƙule mata tare da raɗaɗi wanda tana jin kamar baza ta iya jurewa ba, musamman in ta ga gibtawar sa, tana son zubar da hawaye ko don ta samu salama amma inaa; ta ƙi bari hawayen su zubo mata, yayinda take kokarin hana kanta kowanne irin tunanin sa ne, a zahiri zaka yi tunanin babu shi a ranta ne sam, domin rayuwarta take yi normal cikin walwala da farin ciki babu komai da ke nuni da ta damu dashi, amma a cikin zuciyarta ita kaɗai ta san azaban da take sha, bata da sukuni ko kaɗan, Da yawan lokuta don shi take tashi tayi Ibadan dare, ada bata da burin da ya wuce tayi addu'ar da Allah zai amsa don ta same shi, amma a yanzu, burin ta kawai ta samu sauƙi daga makauniyar soyayyar da ta riƙe mata ruhi, Allah ya cire mata shi gaba ɗaya a ranta, addu'ar ta kenan a kullum Allah ya cire mata son bawan nan nasa ya maye mata da alkhairin sa, Amma sam babu ci gaba kullum jiya iyau, sauƙin da ta samu kawai yanda yanzu ba ta iya bayyana soyayyarsa a fili kamar yanda tayi haukan sonsa a baya, yanzu tana iya shanye duk wani abu a cikin ranta ba tare da kowa ya san meye a zuciyarta ba, Wannan shi ne ci gaban da ta samu Har su Ammee suka gama hutun sati ɗayansu suna shirin tafiya, wanda a ƙarshen ziyarar su ne suka je gidan su can family house din su, shima wannan karon har da Momy ta bi su tunda gida ne, a can suka wuni sai dare Babban Yayan su Momy ya kawo su, Don shi ne kaɗai namiji a cikin ɗakin su, shima bai cika zama a nan ba yana can Kaduna yana aiki, but Matansa guda biyu ne, ɗaya tana zaune a nan Kano tunda ita ce Uwar gida tana da yara manya, kuma ta aurar da Mace ɗaya da Maza biyu, ɗaya kuma Amaryan wacce bata fi shekaru huɗu da auren ta ba, Yaron ta ɗaya ita ce take zaune a Kaduna inda yake aiki Alhamdulillah Familyn suna zaune lafiya, don in ka ga ahalin baza ka taɓa cewa akwai ƴan uba ba, suna zaune lafiya sun haɗe kansu kamar yanda tun farko Mahaifinsu ya koyar da su Su Ammee suna gama hutun su suka wuce gaba ɗaya, Maryamu kamar ta bi su don bata so su Aakifah su tafi ba, Amma babu yadda zata yi kasancewar hutun sati Uku ne kacal, can ma zasu wuce dangin Abee ɗin su ne suyi hutun a can shine dalilin da Ammee ta wuce dasu, amma ba don haka ba zata bar su ne suyi hutun gaba ɗaya Bayan tafiyar su; Momy tare da Maryamu suka shiga kitchen suka soma shirya abincin dare, suna yi suna taɓa hira Momy tana tambayarta a kan harkan karatun nata, Nan kuwa ta zauna tana ta bata labari tunda Maryamu akwai son zance in ta samu wuri, bakin ta ba ya shiru, Har labarin kammala koyon computern su take bata, don yanzu sun gama komai Abee yayi musu alƙawarin siya musu computer, yanzu kuma sun koma koyon makeup ne Suna cikin girkin ne su Hanif suka dawo gidan, Dama su Dady suna zaune a falon; shi da Sadiq da shi yake harkan karatun sa a cikin laptop, Hanif ne ya wuto kitchen ɗin after sun gama magana da Dady a kan aikin nasu, yabar SHAREEF a can suna ci gaba da zanta wa Lokacin da ya shiga yake kiran sunan Momyn da cewan, "Weldon Mom, ashe kuna nan? Tunda na ji ƙamshi da ɓuruntu nace bari in taho." Ya ƙarisa wurin yana duban tukunyan da ta buɗe tana juyawa "Ina nan Hanif, muna aiki da Maryam, ai yanzu ma zamu kammala." "Sannu da zuwa Yaya Hanif." Maryamu tayi maganar cikin fara'a tana dakata wa daga fere doyan da take yi While shi kuma ya sanya hannu ya ɗauki wuƙan da faɗin, "an gaishe ki My sister, su Aakifah sun tafi sun bar ki da kewa ko?" Dariya tayi tace, "wlh kuwa Yaya, amma tunda ga ku na san zaku maye min gurbin su." Sai tayi saurin miƙa hannu zata amshi wuƙan da faɗin, "No Yaya kar ka ɓata hannun ka kawo don Allah." Ɗan hararanta yayi yace, "wa yace miki ban iya ba wai? Tambayi Momy ki ji, tun ina ƙarami Ni nake taya ta ayyuka, a can England Ni nake komai ba na siyan abinci." Murmushi kawai Momy tayi tana canza maganar da faɗin, "ina SHAREEF ɗin?" "Yana falo Momy." Maryamu kama wani aikin tayi tabar masa wannan, Suka ci gaba da ɗan taɓa hira tsakanin su, har Hanif ya gama fere sauran doyan, Ita kuma Maryamu ta wanke ta zuba a tukunya ta ɗaura a kan wuta Hannunsa ya wanke sannan ya juya ya fita ya bar su, Sai da suka gama before suka shirya komai a saman Dinnig, time ɗin an kira sallan magriba ma, Momy tabar wa Maryamu sauran ayyukan ta wuce daki yin Sallah, While Maryamu kuma sai da ta gama kimtsa komai ta share kitchen ɗin before ta wuce dakin ta, Koda ta shiga, toilet ta afka tayi wanka ta fito, ta nemi riga da wando na fakistan masu sauƙin nauyi ta saka, wandon mai ruwan zuma ne burgujeje wanda za a iya saka mutum a ciki, sai milk color na rigan mai design ɗin kalan zuma, Ɗankwalin ɗan karami ne, shiyasa bata yi amfani dashi ba, ta samu hula baƙa ta rufe danƙararren gashin ta wanda ya daskare sabida rashin kitso, domin har yanzu Maryamu ba ta ƙaunar abun da zai taɓa mata kan nan nata, da yawan lokuta Ammee take mata faɗan rashin gyara shi tayi kitso, amma da ta fahimci yadda take ciwo duk sanda aka taɓa mata, don haka shiyasa ta dena matsa mata, Ita kanta Maryamun abun yana damunta yanzu, don tana son ta riƙa gayu da gashin nata kamar yanda su Yusaira suke yi, amma babu hali, da zaran ta taɓa kan da sunan gyara wa ya dinga mata ciwo kenan, sai ta kwana ta wuni tana zazzaɓi, wani lokacin har ta kwanta jinya tsaban azaban ciwo, Duk da haka yanzu ba kamar baya bane, tana ƙoƙarin ta gyara jifa-jifa duk da ba a mata kitso, sai dai ta wanke kawai haka nan ta ɗan saka mayuka masu ƙamshi, dama can gashin ta akwai shegen ƙarfi, kuma ba shi da tsawo sai yawa, dalilin da yasa in ya cinkushe take shan bak'ar wahala kenan After ta gama shirya wa ta saka slippers ta fice zuwa Falo Su Dady basu dawo ba sai da aka yi sallan isha'i sannan suka shigo While SHAREEF kuwa tunda aka yi magriba ya bi ta ƙofan baya ya koma ɗaki, Bai fito ba sai da ya ji an kira sallan isha'i sannan ya koma masallacin, Koda suka idar shine ƙarshen shigowa gidan Tun da ya shigo Falon Maryamu tayi masa duba ɗaya ta ɗauke idanunta a kansa, Sam ta ƙi kallon inda yake bare su haɗa ido, amma a ranta tana mamakin yanda ya sauya ya rame sosai kamar ba shi ba, ko zuwan su bai kai raman yanzu ba Shi kuwa ganin akwai Maryamu a wurin, sai bai zauna ba ya wuce wurin Dinnig, da kansa yayi save ya soma cakalar abincin da sam ba ya masa dad'in ci, kawai turawa yake yi amma hankalinsa ba ya wurin, yana can duniyar tunanin da ya saba yanzu "Dady zan je Katsina a kan gwangilan da na faɗa maka zamu karɓa, Ni zan je mun rigada mun yanke shawara da Bro." A cewar Hanif da ke duban Dadyn wanda yake gefen sa Dady yace, "Alhamdulillah, to Allah ya kaimu rai da lafiya ya nuna mana aron kwana." Dukkan su suka masa masa, Yayinda Momy take tambayarsa, "da yaushe ne zai tafi? Kuma kwana nawa ne?" "Da safe ne zan wuce, just one day zan yi." "To mai kake so in haɗa maka wanda zaka tafi dashi?" "Mom babu komai, kwana ɗaya ne fa, bazan jima ba ki bar shi kawai." Dady da ke murmushi yace, "dama dai SHAREEF ne, shine wanda zai buƙaci wani abun, amma ba Babana ba, duk inda ya tsinci kansa yana ƙoƙarin yin rayuwa irin nasu. Yauwa. nace ya maganar mu na baya a kan nemo Mata Babana, ka samu ko har yanzu ka manta da zancen ma?" Dariya yayi yana sosa ƙeya cike da kunya, "No Dad, ina tune wlh." "Ok akwai daddaɗan labari kenan? Don daga ganin bakin nan naka yana motsi akwai labari?" Dariya kawai yayi bai iya cewa komai ba "Faɗa mana muna sauraron ka, aina yarinyar take? Don ba na son a wuce dogon lokaci ban aurar da ku na huta ba, shi wancan Babban kawai din; ga shi da Mata har biyu amma har yanzu babu wata wacce ta tare." "Dady yarinyar da muka taɓa taimaka mata ne wacce ka basu gida a Hotoro." Da mamaki Dady yace, "wai yarinyar nan Kurma ko?" Kansa ya gyaɗa mishi ba tare da yayi magana ba, duk da fargaba ce sosai a ransa gudun kar su ƙi amincewa Shiru Dady yayi shima bai ce komai ba Ita kanta Momy mamaki ne ya cika ta, tace, "Hanif, yanzu kurman ne zaka aura? Kallonta yayi cikin sanyin murya yace, "Mom tana da hankali ne shiyasa, yarinya ce mai tarbiyya shine abun da ya ja hankalina gare ta, kuma mun fahimci juna sosai wlh." Girgiza kanta tayi tace, "Yaro Yaro ne, amma ina gamin ka da Kurma Hanif? Koda kun fahimci juna ai bata dace da kai ba, saboda matsalar a nan gaba ake gudu, taya ya zaka auri wacce ba ta magana?" Dady yace, "ba batun wannan ba Dija, ai itama Allah yayi ta, baza mu hana sa abun da yake so ba, ta Yiwu shi nashi ƙaddaran kenan auren irin ta, amma before mu yanke hukunci yakamata ka sake nazari da kyau Babana; gudun abun da zai je ya dawo, don ba jima wa za a yi ba, muddin nayi bincike auren kawai za a yi a haɗa dana ɗan uwanka in Matar tashi ta dawo." Sai yanzu Hanif ya ji sanyi a cikin ransa, nan da nan murmushi ya bayyana a kan face ɗin sa yana faɗin, "Insha Allahu Dad." Momy bata yi magana ba tunda ta ji abun da Dady yace, sai tayi shiru kawai duk da har ranta ta damu da jin wacce ɗan nata zai aura, amma kuma kamar yanda Dady yace ne, in ƙaddaransa ne auren ta dole su bar shi yayi, baza su matsa mishi ba Duk abun nan da ke faruwa SHAREEF na sauraron su daga inda yake amma bai ce komai ba, sai da Dady ya kira sa sannan ya miƙe ya taho wurin Bayan ya zauna a gefen Sadiq; Dady yace mishi, "to ka ji muna maganar auren ɗan uwanka, in har nayi ƙwaƙkwaran bincike babu matsala za a haɗa auren da naka, yaushe ne ita yarinyar zata kammala karatun nata?" Shiru SHAREEF yayi na ɗan wani lokaci kamar bazai yi magana ba, sai kuma can ya buɗe baki yace, "few months ne Dady." "To Alhamdulillah Allah ya kaimu lokacin, sai ku zaɓi kowanne gida da zaku zauna, but a kusa nake son zaman ku; kunji ko?" Hanif ya amsa mishi da baki, while SHAREEF kansa kawai ya ɗaga Maryamu tana zaune tana jin duk abun da ke faruwa, amma ta kasa ɗago kai saboda gudun a gane halin da take ciki, Momy ma sai kallonta take yi tana son ta gane wanne yanayi ne a tare da ita, Amma ko kusa bata ɗago kai ta kalle su ba, don ba ta bukatar kowa ya gane yanayin ta, Sai ma tashi tayi ta wuce wurin Dinnig ta zauna tana zuba abincin ta, Amma yadda zuciyarta take buga wa natsuwarta tana neman ta ƙwace mata, ƙarfin hali kawai take yi da hana bayyanuwar tsantsan tashin hankalin ta, haƙiƙa tana kaunar SHAREEF sosai, amma ya rigada ya yi mata nisa, nisan da baza ta taɓa cin masa ba, tabbas dole ta ba wa kanta haƙuri ta danne komai ya wuce, a yanzu babu abun da take so sama da ta san matsayin ta, baza ta iya jure zama a haka tana kallonsa da wata bayan ita ba, tana da matukar kishi, ta gummaci ta rabu dashi in dai a yanzu ne, rabuwa na har abada kuwa Suma su Momy abincin suka koma saman Dinnig suna ci, While SHAREEF yana zaune a kan dogon kujera yayinda ya ƙura wa TV ido, a zahiri tamkar kallon yake yi, sai dai ba haka bane, remote yana hannunsa yana canza channels amma ba ya gane komai, Jima wa kaɗan kuma ya miƙe yayi musu sallama ya haura sama Maryamu a sace ta bi sa da kallo har sanda ta ga ya ƙule mata, before ta ɗauke kanta tana jan dogon numfashi mai ƙarfi Momy ce kadai ta kula da halin da take ciki, girgiza kanta kawai tayi tana kawar da kai daga kallonta, sai yanzu ta ƙara tabbatar wa har yanzu SHAREEF yana a zuciyar Maryamu, amma yadda ta sauya tana danne komai a zuciya; ba ƙaramin burge ta tayi ba, ko banza yanzu ta nuna tana da aji.*** The following day. Maryamu sai kusan ƙarfe goma ta tashi, tun tashin ta da asuba ta koma sai yanzu ta farka, Tayi wanka ta saka doguwar rigan atamfa mai kalan purple da kwalliyar star mai kalan ruwan madara, doguwar hannu ne da rigan mai bottles a ƙarshen hannun, haka ma gaban rigan an sanya two bottles; yayinda wuyan ke da Coller, Cif tayi mata rigan daga sama while ƙasa kuma ta buɗe, Sai da ta ɗaura ɗankwalin before ta wuce ta nufi Falo Babu kowa sai Sadiq a Falon, Yana kwance a doguwar kujera wayansa a hannun sa yana faman latsa wa Wurin sa ta nufa da fara'an ta ta kira sunan sa, "Yaya Sadiq good morning?" Sai da ya ɗago ya dube ta before ya miƙe zaune, face ɗin sa da murmushi yace, "Morning My lovely sis, kin tashi lafiya?" "Alhamdulillah Yaya." Ta amsa mishi tana zama gefen sa "Sai yanzu kika tashi har Yaya Hanif ya tafi." "Eyya ban ji daɗi ba, na so mu sake yin sallama, but zaka ara mun waya ai na kira shi, Ina Momy?" "Momy tana sama ita da Dady." "Yauwa Yaya Sadiq, Please ina son zuwa shopping don Allah ka kaini, There are things I need to buy, and I want you to buy me a phone please, na gaji da zama haka nan nima na ƙosa in riƙe tawa since na zama big girl." Dariya ta ba Sadiq, sai kuma ya ji daɗi musamman da ya ji tana turanci ba kamar haukan ta a baya ba, yanzu ta ɗan kware ba shirmen da ta saba yi ba, ba ƙaramin burge sa tayi ba, sai yace, "Ni dai bani da kuɗi Maryam, but mu bari Dady ya fito sai ki tambaye shi, inyaso ko zuwa after azuhur ne sai mu je shopping ɗin, ai bazai yiwu a bar big girl babu waya ba." Dukka suka yi dariya sabida ta gane tsokanarta yake, But sai tace, "thanks sweet Bro, amma yaushe ne zaka tafi karatun ka? Na ji Momy tana maganar da Ammee lokacin kafin su tafi." Sadiq yace, "ba yanzu ba ai, maybe before ki tafi or after kin tafi, just few weeks." "Allah ya kaimu lafiya." "Amin ya Allah". *** _____Koda Maryamu ta faɗa ma Momy zasu fita shopping da Sadiq, bata hana su ba, ita da kanta ma ta basu kuɗin, Dady ya ƙara musu ya bada kuɗin wayan tare da nasu Aakifah, yace, "a siya har da su." Maryamu sai murna take yi, ba ƙaramin daɗi ta ji ba, shiyasa da suka je supper market din, ita da kanta ta zaɓi wayoyin dukka iri ɗaya, but ta bambanta color din rigan wayan, ita nata sky green ne domin kalan ne ta fi ƙauna, suma sai ta ɗaukar musu nasu favorites ɗin, Suna cikin siyayyan ne tayi gaba tana neman abun da zata ɗauka tana tura basket da take zuba siyayyan nata Sai ga wani saurayi ya zo ya sha gabanta yana mata magana Maryamu tunda ta kalle shi sau ɗaya ta ɗauke idanunta a kansa bata sake kallon sa ba, sai dai sauraron sa da take yi tana duban abun da zata ɗauka Sadiq daga can nesa ya hango su, Saurayin na kokarin jan mata basket ɗin wai zai taya ta ɗauka, nufo wurin yayi yana duban sa da cewan, "excuse me Oga, ya haka zaka tsaya da Matar aure kana shishshige mata?" Da mamaki saurayin yake kallonsa, sai yace, "haba, ai na ga ita kaɗai ce kuma bata yi min kala da Matar aure ba." "To a goshin ta za a rubuta ne?" Sadiq yayi maganar cikin ɗaure fuska, har yana saka hannunsa ɗaya a aljihu tare da goce tsayuwar sa irin na isassun Mazan nan, ya ƙara da faɗin, "don Allah kabar nan wurin in ba so kake in maka duk abun da ka siya da kuɗin ka ba, Matana ce ita, zaka iya tafiya yanzu." Yanda Sadiq ya tsare sa da ido babu alamun wasa a tare da shi, bare yanda ya ganshi jibgege shiysa bai yi musu ba, a tunaninsa da gasken shine Mijin nata, hakan yasa ya ba shi haƙuri ya wuce a wurin da saurin sa Mai Maryamu zata yi in ba dariya ba, ta kasa riƙe dariyanta sabida abun da Sadiq yayi Yayinda shima yake taya ta yana ƙara gyara gaban rigansa sai ƙwambo yake yi, "yo ya kika ga acting ɗin nawa? Wlh ya ɗauka Ni Mijin naki ne fa." Dariya tayi ta ɗaga masa hannu alamun jinjina tana cewa, "Yaya Sadiq wlh ka burge Ni." "To in ban da abun shi ɗan rainin wayon, an gaya masa kowa ake gani a hanya a kula? To an riga sa wannan, ina wuri baza a ci wa auren Yayana mutunci ba." Jin hakan yasa Maryamun bata sake magana ba, sai ma gusar da dariyan fuskarta tayi tare da canza zancen nata tana yi tana duba abun da zata dauka A haka suka gama siyayyan su; tunda shima Sadiq ya siya wasu abubuwa nasa da yake bukata in zai wuce England, After sun biya suka koma Mota, ya ja suka bar wurin, suna ɗan taɓa hira kiran SHAREEF ya shigo wayansa, Rage gudun motan yayi sannan ya amsa call ɗin Daga can side ɗin SHAREEF yake tambayarsa inda yake a yanzu? Yace, "muna kan hanya ne zamu koma gida." Umarni ya basa a kan, "ya biyo Company yanzu yana neman sa." Bai tsaya jin ta bakin sa ba ya katse kiran Maryamu kuma bata san da waye yake wayan ba, sai da ta ga ya karya kwana ba hanyar da suka biyo ba, ta kalle sa tace, "wai ina zamu je ne Yaya Sadiq?" "Companin mu zamu je, yanzu da Yaya SHAREEF na gama waya yace in je in same shi." Shiru tayi bata sake yin magana ba har suka isa can, Tunda suka shiga cikin katafaren Companin take faman kalle-kalle gunun sha'awa, ba karamin burge ta yayi ba musamman yanda ta ga girman sa, lallai sai yanzu take ƙara jinjina matsayin Dady da yawan kuɗin sa, Allah ya basa dukiya mai yawa ga shi har wasu suna cin arzikin sa, tana godewa Allah da itama ya tsamo ta a cikin talauchi cikin wancan ƙauyen; ya zamana itama zata samu wannan farin cikin, zata yi rayuwa cikin daula, in ta tuna hakan tana farin ciki ba kaɗan ba, ko banza yanzu tayi gaba Koda Sadiq ya nemi ta fito su je tare, sam ta ƙi yarda, tace mishi, "ya je ya shiga tana jiran sa a nan." Wayansa ta amsa ta riƙe tana faman latsa wa Almost ten minutes sai ga su sun dawo shi da SHAREEF ɗin, wanda yake riƙe da cikinsa da ke masa ciwo, dama dalilin kiran Sadiq ɗin kenan ba ya jin daɗi, kuma bazai iya tuƙi ba, yana bukatar ya koma gida ya kwanta ya huta, Sadiq shi ya riƙo mishi Jakan sa da wayansa suka taho Maryamu duk bata ankare da zuwan su ba, hankalinta yayi gaba wajen buga Game, sai ji tayi an buɗe ƙofan side ɗin ta, ɗago idon da zata yi suka shige cikin na SHAREEF; wanda shima yayi turus a wajen bai yi expecting ganin ta ba. [12/04, 3:38 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱         *SHAREEF*              _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE17* _____Kamar yanda ya kasa ɗauke ido a kanta; haka zalika itama ta kasa janye manyan idanuwanta da ta ware su bisa cikin nasa, tamkar an sanya musu mayen ƙarfe haka kowannen su yake jin wani abu na rinjayen su zuwa cikin idanunsu, wanda hakan ne yasa suka kasa janye kallon da suke yi wa juna, Yayinda bugun numfashin su yake tafiya cikin sauri-sauri da wani irin yanayi Sadiq shi ya katse musu halin da suke ciki, yayinda yake furta, "Maryam, ki bama Yaya SHAREEF wuri ya zauna a nan, sai ki koma baya." Take ta rufe idanunta tana buɗe wa a wani yanayi, sai dai sam babu walwala a kan fuskarta take kallon Sadiq da har ya zauna a mazaunin sa, sake tsuke baby face ɗin ta tayi a gadarance tace, "a kan me zan tashi in koma baya; after I am the one who saat here? Meyasa shi bazai shiga can bayan ya zauna ba?" Sai ta gyara zaman ta tana ƙara wa da faɗin, "I have nowhere to go." Ba Sadiq ba; hatta SHAREEF mamakin furucin ta da ƙarfin halin ta ne ya cika su, wanda yasa kowannen su ya kasa magana suka zuba mata ido suna kallon ikon Allah, musamman ma SHAREEF da yake tsananin mamakin yarinyar da har ta iya gaya masa magana haka Ita kuwa ɗauke kanta tayi tana hura hanci cikin isa da gadara, har da wani harɗe ƙafafu tana kaɗa su, wadda har cikin zuciyarta ba ƙaramin ƙarfin hali tayi ba har ta iya jurewa tayi maganar, musamman da take jin hucin sa a kusa da ita, tsoro da fargaban abin da zai biyo baya ya cika ta, zuciyarta na buga wa fat-fat kamar zata zillo waje SHAREEF kuwa a yanayin da yake ciki sam bazai iya magana ba, ransa ya ɗan ɓaci don ganin rashin kunyar da Maryamun take shirin mishi yanzu, sam bazai iya jurewa ba, don ya gwada mata ba ta gabansa shiyasa ya saka hannu ya finciko ta waje sai ga ta warwas a ƙasa ya jefar da ita Ihu ta fasa sabida bige hannunta da tayi, da sauri ta ɗago gwiwar hannunta tana kallo ko ta ji ciwo, take hawaye suka cicciko a cikin idanuwanta, ta bi SHAREEF ɗin da kallo cikin tsananin bakin ciki da takaici, ganin sun haɗa ido yana kallonta; yasa tayi ƙoƙarin tsayar da hawayenta batare da ta bari sun zuba ba, mugun kallo ta watsa mishi cikin baƙin ciki tace, "Allah ya isa ban yafe ba wlh, mugu azzalumi mai baƙin hali..." Bata iya ƙarisa zancen ba saboda ganin yayi yunkurin fitowa, shiyasa ta mike da sauri tana shirin gudu wa Wani irin murɗawa cikin sa yayi, maransa ta riƙe ƙam shiyasa da sauri ya koma ya zauna yana dafe da cikin sa, ga azaban ciwo ga tsananin ɓacin ran da Maryamu ta sanya shi saboda jin zagin da tayi masa, ya kasa ɗago kai balle ya kalle ta sai faman cije laɓɓa yake yi yana riƙe da cikin nasa Sadiq kuwa fitowa yayi yana kiran Maryamu da har tayi nisa, "Maryam, ki zo ki hau mota mu tafi don Allah." Juyawa tayi ta kalle sa, a fusace tace, "bazan hau Motan nan ba in har da wannan mutumin a ciki, zan wuce in samu napep." Tayi maganar tana ƙarisa juya wa zata bar wurin Amma sai Sadiq ya sake kiranta yana cewa, "ta dawo su tafi, idan Momy ta san cewa ya barta a nan zata saɓa mishi. Please Maryam zo ki hau don Allah." Ya ƙare maganar da roƙon ta yana nufan inda take, Hannunta ya riƙe yana janyo ta, a hankali ƙasa-ƙasa yake cewa, "wai ba ki da hankali ne Maryam? Yaya SHAREEF kike ma rashin kunya? Ko kin manta abun da na faɗa miki a baya ne?" "Ban manta ba, kana ganin da da yanzu ɗaya ne Yaya Sadiq? Wa ya faɗa maka ina sonsa?" Sai ta ja dogon tsaki tace, "wlh zan nuna masa ainihin color na, in har zai wulaƙanta ni Ni kuma na soma mishi rashin kunya kenan, sai dai ya kashe Ni, ba na tsoron sa; ba na sonsa ma yanzu, mai zan yi da mugu?" Dariya ne ya so kufce wa Sadiq sabida yanda ya ga tana maganar a zuciye kamar SHAREEF ɗin ne a gabanta, shiru yayi kawai yana kallonta batare da ya iya furta komai ba, yanzu ya tabbatar da cewan Maryamu ta sauya, anya ma akwai soyayyar SHAREEF ɗin a zuciyarta ko kuma maganar nata gaskiya ce? Tirƙashi! Buɗe mata bayan Motan yayi yace, "ta shiga." Sai da ta ja guntun tsaki sannan ta shige tana faman hararan bayan SHAREEF da bai san ma tana yi ba Hannu Sadiq yasa ya ranƙwashe ta yana jan mata kunne, yayinda yake mata gargaɗi da hannu a kan ta kiyaye yana nuna mata SHAREEF ɗin Kwaɓe fuska tayi tana faɗin, "wayyo da zafi fa Yaya Sadiq, wlh zan rama." Tsawa SHAREEF ya daka masa, "Sadiq, ubanka kake yi a wurin baza ka zo ka tuƙa mu tafi ba?" Da sauri ya rufe mata murfin ƙofan yana zagaya wa ya shiga mazaunin driver, yayinda ya kalli SHAREEF da ya kwantar da kansa saman kujera idanunsa a rufe yana jan numfashi alamun ba ƙaramin jin jiki yake yi ba Fuskar nan har tsatstsafo da gumi take yi, ya haɗe rai babu ɓurɓushin fara'a a tare da shi, Ba ƙaramin ɓacin rai bane a tare da shi, ji yake yi tamkar ya shaƙo Maryamu ya wanka mata mari, abun baƙin cikin kamar wannan yarinyar take iya gaggaya masa maganganu har da masa Allah ya isa? Ga kuma ƙunƙunan ta da yake faman ji. Lallai dole ya koya mata hankali ya saita mata gabas tunda ya ga alamun kanta rawa yake yi, ta je ta koyo iskanci zata sauke mishi, har yanzu bata isa kallo a wurin sa ba, sauƙin ta ɗaya sabida halin da yake ciki ne; wanda sam ko magana bazai iya yi ba sabida jigatan da yayi, shiyasa ya kasa ɗaukar mataki a kanta Har sun iso cikin anguwan su a bakin titi akwai wani private hospital, wanda a nan ne SHAREEF yake zuwa ana duba sa in irin wannan ciwon nasa ya tashi, kasancewar Likitan Abokinsa ne sun saba, shiyasa yake kai mishi matsalar sa don bazai iya zuwa kowanne asibiti ya faɗa abun da ke damunsa ba, in fact ma ko asibitin da suke zuwa ƴan gidan su bai sake zuwa ba tun lokacin da aka kwantar da shi, Cikin asibitin yace ma Sadiq, "ya shigar da shi." After yayi parking ya fito, While Sadiq ɗin shima ya fita da sauri ya zagaya ya riƙe shi, a haka suka ƙarisa cikin asibitin suka bar Maryamu a wurin tana kumbura tana sacce wa, yayinda ranta yayi mugun ɓaci sabida abun da SHAREEF yayi mata, sam a yanzu bata ji tausayinsa ba duk da ta ga halin da yake ciki, sai ma kwantar da kanta da tayi idanunta sun cika da hawaye ta hana bayyanar su a waje, Wai wanne irin ƙaddara ce ta sanya ta sanin wannan mutumin? Sam bai da tausayi bai da ragowar sa, duk da ada ta shanye wulaƙancin sa, a yanzu kuwa sam baza ta iya ba, ko me zai faru zata jure binne soyayyarsa domin itama ta nuna masa ƙiyayya ƙiri-ƙiri kamar yanda yake nuna mata, baza ta taɓa bari ya ƙunsa mata baƙin ciki ita kaɗai ba, dole shima sai ya ɗanɗana, wlh baza ta ji tsoron sa ba in har bazai fasa wulakanta ta ba, a yanzu ta wuce wulaƙanci domin jin ta take yi dai-dai da zamanin sa, A fili ta furta, "SHAREEF sai na koya maka hankali wlh, mugu azzalumi mara imani, sam baka da imani." Sai kawai ta fashe da kuka sabida tuƙuƙi da baƙin cikin har yanzu tana jin soyayyarsa a ranta, "Ya Allah ka cire min wannan bawan naka a zuciyata, ban san wanne laifi na aikata ba ya Allah ka jarabbe Ni da wannan mummunar ƙaddaran da zai zama ajalina, ina dana-sanin sanin bawan nan naka, ya Allah nima ka rama min irin abun da yayi min." Kuka sosai take yi kanta na saman cinyanta, Sai da ta ɗauki lokaci before ta sanya hannu ta soma share hawayenta sabida alkawarin da tayi wa kanta ta dena zubar da hawaye sabida shi, bai cancanci tayi mishi kuka ba tunda bai da imani, Sai da ta gyara face ɗin ta sannan ta sake kwanciya tana jiran isowar su, yayinda a zuciyarta tunani ne fal tayi shiru tana sauraron bugun numfashin ta. *** _____A can ciki kuwa; SHAREEF shi kaɗai ya shiga cikin office din don kar Sadiq ya san mai zai yi, yace masa, "ya jira sa a nan." Ya shiga ya samu Doctor ɗin a ciki yana faman aiki Yana ganin sa shima ya ajiye bairo din hannunsa tare da kiran sunan sa Zama SHAREEF yayi daƙyar yana faman cije laɓɓa "S. Ahmad kar dai a ce ciwon ne kuma?" "Yes Doctor, ya matsa min ba na samun sukuni yanzu ko kaɗan, haka kawai yake tashi min, magungunan ma da nake sha ba sa min aiki, Please help me ka taimaka min da wasu masu karfi da zai sa na rabu da wannan jarabar." Kallonsa yake yi cike da tausayinsa, sai yace, "solution ɗaya ne fa nace maka S. Ahmad, shine ka nemi Mata kayi aure wannan ne hanya ɗaya da zaka rabu da wannan cutar, domin a kullum ƙaruwa take yi idan kana yawan ciwon nan karshe zai haifar maka da wata matsalar ne na daban, ciki kuwa har da na rashin haihuwa, ba a son sha'awa yana kwantar da Mutum sabida nan gaba abun yana zama wani ciwon daban ne, ina ga ka nemi Mata kawai kayi aure tunda Allah ya hore maka, kana da ni'imomin da kowacce Mace a duniya zaka iya samun ta cikin sauƙi." Shiru SHAREEF yayi yana faman cije laɓɓa, ya san cewa Doctorn bai san da yana da Mata ba a yanzu haka, amma bata da amfani tunda ta ƙi farin cikin sa, kuma bazai iya faɗa masa ba, shiyasa ya gyaɗa kansa a lokacin da ya gama ba shi wasu shawarwarin daban, yace, "zan yi insha Allahu, amma yanzu ka duba Ni ka bani wasu magungunan wanda zasu yi min Please." "Ok ba damuwa." Likitan yafaɗa yana miƙe wa tare da zagayowa wurin sa, Duba sa ya soma yi before ya ɗauki waya ya kira wata staff Bayan ta shigo ta risina tana gaishe da Doctorn, idanunta a kan SHAREEF duk da ba ya kallonta; amma tuni kyawun sa ya ɗauke mata hankali har ba ta jin ma mai Doctorn yake cewa, Sai da ya kira sunanta tukunna ta mayar da hankali a kansa da sauri tana cewa, "na'am Sir." Harara ya watsa mata yana cewa, "common zo ki amshi wannan takardan ki amso min magungunan ciki." "Ok sir." Ta amsa da sauri tana nufan inda yake, Takardan ta amsa sannan ta nufi hanyar fita tana sake satan kallon SHAREEF da bai san tana yi ba. Bata ɗauki lokaci ba ta dawo da magungunan da ya rubuta mata, tare da allurai guda uku, Ta miƙa masa cikin girmamawa, Har wannan lokacin idanunta a kan SHAREEF, musamman yanzu da ya ɗago face ɗin sa tana kallonsa sosai, ba karamin fizgarta kyawun sa yayi ba, ji take yi kamar ta tsaya ta ci gaba da kallonsa tsaban burge ta da yayi, balle yanda ta ga yana yamutsa fuska kamar sai yi kuka sai cije laɓɓa yake yi; ba ƙaramin kyau hakan yayi masa ba kamar wani shagwaɓaɓɓen Yaro, Ba don ta so ba ta fice a cikin office ɗin tana jinjina baiwa da kyawu irin nasa, tana jin dama ita ce da wannan tabbas da ta more Miji (Bata san kyan ɗan maciji bane😏) Doctor miƙa masa magungunan yayi wanda ya zuba su a leda ya zari allura ɗaya, yake cewa, "ga magungunan nan sai ka riƙa sha safe da dare, but ka bi ƙa'ida S. Ahmad don suna da karfi sosai, and yanzu wannan alluran zan yi maka shi zaka ji relief in short time, akwai biyu a ciki gobe za a yi ɗaya haka ma jibi, insha Allahu zaka ji sauƙi babu wata matsala, sai dai ina ƙara baka shawara ka yi aure don Allah, idan abun yayi karfi babu maganin da zai yi masa wlh." Jinjina kansa kawai SHAREEF yayi, yayinda ya rufe idanuwansa ya jinginar da kansa a jikin kujerar da yake zaune, shi kaɗai ya san irin azabar da yake ji na game da ciwon nan Tasowa Doctorn yayi ya buƙaci ya ba shi hannun sa, Batare da ya buɗe idanu ba ya miƙa hannun har aka yi masa bai motsa ba, Daga nan ya ci gaba da ba shi wasu shawarar yana tausan sa a kan hanya mai ɓille wa Bai san SHAREEF jin sa kawai yake yi ba, shi kansa damuwarsa kenan ya rasa yanda zai yi da matsalar Haseena, tabbas lokaci yayi da zai nema wa kansa mafita, amma zai ƙara ƙasƙantar da kansa ko zata amince da bukatunsa yanzu. Sai da ya ɗauki tsawon mintoci before ya tashi suka yi sallama da Doctorn, Yayinda yake jaddada mishi, "ya nemi abinci da zaran ya koma gida ya ci, sabida alluran." Fitowa SHAREEF yayi yana duba inda zai ga Sadiq, sai dai babu shi a wurin, sai da ya soma tafiya har ya kusa barin side ɗin, before ya hango Sadiq ɗin ya taho da sauri ya nufo sa, Saurin riƙo sa yayi yana mishi sannu, Kansa kawai ya ɗaga mishi yana ci gaba da tafiyar a hankali sabida har yanzu maransa a ƙulle take, duk da ya soma jin salama, maybe maganin ne ya soma aiki, Wurin motan suka nufa Sadiq ya buɗe masa ƙofa ya shiga, Sannan shima ya zagaya ya shiga ya kunna Motan Maryamu na jin motsin su amma sam ta ƙi ɗagowa bare ta kalle su, tana kwance a kan kujerar ta rufe fuskarta da gyalen jikinta, tana jin Sadiq na kiran sunan ta amma sam ta ƙi tanka masa, Har suka ƙarisa gida sai da ta tabbatar da yayi packing Motan; before ta miƙe zaune tana buɗe kofan, ledojin siyayyanta ta kwasa ta fita ta rufo motan, ko juyawa bata yi ba tayi cikin gidan ta shige Sadiq kuma shi ya zagayo ya buɗe wa SHAREEF ƙofan sabida ganin ya ƙi fitowa, yace, "zaka iya tafiyan ko in taimaka maka?" Sai lokacin ya buɗe ido, wanda ya rufe su tun shigansa cikin motan, sun ɗan kaɗa alamun yana cikin wani hali, kansa ya girgiza masa alamun a'a, yayinda ya zuro ƙafafunsa waje ya ƙarisa fice wa, ledan maganin yana hannunsa ya nufi cikin gidan While Sadiq kuma sai da ya tsaya daukar masa Jakansa da wayansa, sannan ya haɗa da nasa ledan na siyayya; sannan ya bi bayansa Babu kowa a falon da SHAREEF ya shiga, don haka kai tsaye sama ya haura ya wuce dakin su Shima Sadiq ya bi bayansa da jakansa, bayan yakai masa ya saka shi ya dauko mishi ruwa, Amsa mishi yayi ya fita zuwa downstairs, da Momy ya ci karo ta fito daga ɗakin Maryamu, Da sauri yace, "Mom Yaya SHAREEF fa bai da lafiya wlh, daga asibiti ma muke tare muka dawo gida." "Subhanallah..! Ok bari in duba sa." Tayi maganar tana nufan saman fuskarta cike da damuwa Shima Sadiq ruwan ya je ya ɗauko masa har robber biyu, kana ya nufi ɗakin da ɗan gudun sa A falo Momy ta tarar dashi kwance a dogon kujera idanunsa a rufe, kiran sunan sa tayi tana ƙarisa shigowa idanuwanta a kansa Jin muryan Momyn ne yasa ya buɗe shanyayyun idanunsa yana kallonta, sai kuma yayi yunkurin tashi a hankali ya zauna Zama tayi gefen sa tana kai hannunta saman wuyansa, da damuwa a tattare da ita tace, "me ke damunka SHAREEF?" Shiru yayi yana kallonta, ganin sun haɗa ido hakan ne yasa ya sunkuyar da kansa, in a cool voice yace, "Mom, zazzaɓi ne kawai, but I'm feeling better." With dissatisfied tace, "ban yarda ba, ko dai ciwon naka ne ya tashi kake ɓoye wa? SHAREEF ba ka jin magana ko? Ka fi son kullum ka riƙa sanya mu a damuwa? Kai kanka baka huta ba muma bamu huta ba, ka ɗaura wa kanka wahala da kanka sabida rashin jin magana, shikenan iyakan namu addu'a ne tunda baza ka ji magana ba, amma ka sani wlh ko don rashin mana biyayya Allah bazai ƙyale ka ba, dole sai ya jarabbe ka, in zaka canza tunani ka canza, in kuma baza ka canja ba ya rage naka, iyakan mu bi ka da addu'a, Allah ya yaye maka, muna nan muna jiran lokacin da zaka cire girman kanka ka dawo kan hanya." Sai tayi shiru da ta kawo nan a zancen ta, Bata sake yin magana ba sabida ganin Sadiq ya shigo cikin dakin Yayinda shima SHAREEF bai ce uffan ba, sai dai ba ƙaramin mugun sanyi jikinsa yayi ba, musamman da ta furta cewan maybe alhakin su ne yake bibiyansa, Idanunsa sun cicciko da hawaye amma ya hana bayyanar su bare har a gani Momy kuma tashi tayi tace, "bari in kawo maka abincin ka nan, Allah ya sawwaƙe." Fita tayi batare da ta jira cewar sa ba Yayinda Sadiq ya ajiye masa ruwan yana cewa, "Yaya ga shi." Guda ɗaya ya ɗauka ya buɗe a hankali, tare da kallon Sadiq ɗin ya ba shi umarnin ya ɓallo mishi magungunan kowanne, Bayan ya gama ya miƙa masa, a hankali ya amsa ya soma afawa ɗaya bayan ɗaya yana sha har ya gama, sannan ya ajiye sauran ruwan yana jingina bayansa da kujerar, sama-sama yake jin jiri yana ɗibansa ƙarfin hali kawai yake yi sai faman cije laɓɓa yake yi yana sauke numfarfashi Sadiq kuma ɗaukar ɗaya ruwan yayi wanda bai buɗe ba, ya mayar a cikin fridge ɗin Falon nasu, sannan ya fice a ɗakin yana rufo masa ƙofan.*** Momy wacce ta sauka ƙasa, ta hangi Maryamu zaune tana faman latsa sabuwar wayanta cike da zumuɗi, Kiran sunan ta tayi tana cewa, "Maryam zo nan ki kaiwa Yayanki abinci a ɗaki." Daga haka ta wuce ta shige cikin kitchen Ita kuma jin abun da Momy tace ne yasa ta ƙi tashi bare ta bi ta, nan da nan ƴar fara'an kan fuskarta ta gushe, tana zaune tana tura baki kamar bata ji mai Momyn tace mata ba Har ta fito ta same ta a nan zaune, ta dube ta da mamaki tace, "Maryam, ko ba ki ji mai nace miki bane?" "Momy wlh ya hana Ni shiga ɗakin sa, Ni ba na son abun da zai haɗa Ni dashi kuma yanzu." Hararanta tayi tace, "zo ki amsa, ya kashe ki in kin je kinji ko? Common zo ki wuce." Ba don Maryamu ta so ba ta tashi ta nufe ta, kuma don kar tayi mata musu ne amma da wlh sai ta gaya mata baza ta je ba, amma duk da haka sai da ta tsuke fuska alamun ba ta son zuwa, Ta amshi tray ɗin da ta shirya masa abincin Momy na bin ta da kallo bata ce mata uffan ba har ta wuce, shiru tayi tana kallon bayan Maryamun har ta ƙule wa ganinta, a ranta kuma tana tunanin ko dai Maryamun ta dena son SHAREEF ɗin ne? Ikon Allah! Kenan. "Allah yasa hakan ne ma." Tayi maganar tana juyawa ta shiga kitchen ɗin While Maryamu kuma bayan ta isa baƙin ƙofan, sai da ta tsaya ta ɓata lokacin ta tana saisaita kanta, sai da ta samu natsuwa sosai tukunna ta tura ƙofan ta saka ƙafafunta ciki, yayinda tayi sallama ciki-ciki babu mai ji sai ita, a nan idanuwanta suka faɗa a kan SHAREEF da ke zaune har lokacin, ya kwantar da kansa idanu a rufe, Bai san da shigowar ta ba har ta isa wurin sa Tana sauke tray ɗin a saman Centre table ya buɗe idanuwansa sabida jin motsi, take a nan idanun suka sauka a kan ƙirjinta da rigan ya zazzago sakamakon duƙawar da tayi, wani irin yanayi ne ya baƙunce sa daga can tsakiyar ƙafafuwansa har izuwa ƙwaƙwalwan sa, take a nan ya ja dogon numfashi yana sake ware idanun a kanta sam ya kasa ɗauke ido daga kallon abun da suka tsole mishi idanu da tsananin kyawun da suka yi masa, Har ta ajiye ta miƙe bai daina kallonta ba yana haɗiyar yawu sabida wani mugun sha'awar da ya tunkaro sa, tamkar ya janyo ta sabida ilahirin jikinta da ya soma zauta shi, Dayake babu gyale a jikinta; kuma ta sauya shigan ta da suka dawo shop, yanzu tana sanye da straight skirt ne ja da rigansa mai santsi, gaban rigan bottles ne but bata rufe na kan ƙirjinta ba, wanda hakan ne ya ba shi damar ganin twins ɗin ta masu ɗaukar hankali da cika gunun sha'awa, wanda nan take suka motso mishi da wutan sha'awarsa suka ɗauke masa hankali har ya gaza janye lumsassun idanuwansa da suka juye don jaraba Yayinda sam Maryamu ta gaza kallonsa bare ta san mai yake yi, illa ma juya wa da tayi zata bar cikin Falon tun sanda ta ajiye tray ɗin, Har takai bakin ƙofa ta jiyo sautin muryansa, Amma ta kasa dakata wa sabida jin abun da yace, Buɗe ƙofan tayi da ninyar fice wa, amma sai ta sake jin ya tsayar da ita, Hakan ne yasa ta dakata na ɗan seconni; before ta juya face ɗinta a tsuke babu fara'a ta narka mishi waɗannan manyan idanuwan nata masu girma da haske da daukar hankali, hannayenta a ƙugu cikin tsiwa da haushin sa tace, "lafiya kake kira na da Kee? Ko baka san suna na bane?" Kasa magana yayi kamar an rufe masa baki, kaifafan idanunta da ta zuba mishi ba ƙaramin saka shi a wani yanayi yayi ba, amma ya kasa ɗauke idanun a kanta yayinda shima babu wannan walwalan a kan face ɗin sa Kallon kallo suke wa juna kowanne da nashi salon, Inda ita tuni ta ja dogon tsaki ta watsa mishi harara ta juya ta ƙarisa fice wa sabida ganin ba shi da abun faɗa Wanda shi kuma ya tsayar da ita ne don ci gaba da kallon surar jikinta, hankalin sa ya gushe batare da ya san abun da ya aikata ba, sai daga baya yake dana-sani musamman abun da ta furta mishi da kuma tsakin da tayi mishi, ba ƙaramin ƙona mishi rai tayi ba yana jinjina ƙarfin halinta da ta koyo har tana iya masa magana irin haka, abun takaicin ma yanda yake jin zuciyarsa tana kwaɗaita masa surar jikinta wani irin mugun sha'awarta yana mamayan sa, a halin da yake ciki sam bazai iya hukunta ta ba, amma ba don haka ba da tuni ta raina kanta ya bi ta ya ci Ubanta, Jirin da yake jin yana ƙara taso mishi, shiyasa ya daure ya ci abincin sosai don ba ƙaramin yunwa yake ji ba. Bayan ya gama ya sha ruwa sannan ya kwanta a nan kan kujerar, Babu jimawa barci ya sure sa cikin kwanciyar hankali tunda ya soma jin sauƙi.*** To kamar wasa kuma sai ya ji sauƙi alamun maganin ta karɓe shi, bai sake jin ciwon ba har washe gari, domin har shirya wa yayi ya nufi wurin aiki a ranar, tare da alluran ya tafi ya wuce wurin doctor yayi masa sannan ya tafi wurin aiki, Sai ƙarfe biyar yanda ya saba tashi haka ya dawo Time ɗin ma Hanif ya dawo daga tafiyar sa, tunda dama kwana ɗaya ne zai yi. *** _____Yau kusan kwana biyar kenan SHAREEF bai yi waya da Haseena ba, abun yana damunsa saboda ko ya kira baza ta ɗauka ba sai idan ita take buƙatar suyi wayan zata kira, To ya gaji da jin shirun ta kuma yana son ya ƙara roƙon ta ko zata amince dashi, domin ba ƙaramin kewarta yake yi ba Yana kwance a ɗakin su lokacin dare yayi, bai tsaya hiran ba tunda suka ci abinci ya shige ɗaki yabar mutanen gidan a falo, wayansa ya dauka ya kira ta har kusan sau uku before tayi peaking, Ya kasa ma magana don bai san mai zai ce mata ba, Sai da ya ji muryanta sannan ya rufe ido yana buɗewa, cike da damuwa yace, "Haseena yanzu kin dena so na ko? Kin gummaci ki ɓata min sabida kinga ina sonki; na damu da ke a rayuwa na kasa cire ki a rai ko?" Shiru ne ya biyo bayan zancen nasa domin ta kasa yin magana, domin a lokacin daƙyar ta ɗauki wayan ma suna tare da Nana suna abun da suka saba, wanda ko gajiya ba sa yi Nishin ta kawai yake ji; da hakan ba ƙaramin ɗaga masa hankali yayi ba, take ya soma jin buƙatar ta a tare da shi, ransa a jagule ya sake kiran sunanta da ƙarfi yana cewa, "wai Haseena mai kike so da Ni ne? Mai nayi miki da zafi haka da baza ki bani haƙƙina ba? Meyasa kika sauya min kike son ganin na mutu da bukatar kasancewa da ke? Don Allah ki bani dama na zo muyi Ko sau ɗaya ne, wlh ina cikin wani hali, a koyaushe bani da kwanciyar hankali, mutuwa zan yi sweetheart; zan mutu ina matuƙar bukatarki." Sai ya marairaice murya kamar zai yi kuka yace, "Please sweetheart help me kar in zauce, ke kaɗai nake so bazan iya haɗa ki da wata ba, bazan iya aikata zina ba." Daƙyar tayi magana a yanzu tace, "dear, Ni fa baza ka samu abun da kake so ba har sai na tare a gidan ka, in fact ma Ni yanzu wannan abun ba ya ɗaɗa Ni da ƙasa, please kayi haƙuri ka mayar da zalaman ka a ciki don baza ka taɓa samun abun da kake so ba, don Allah kar ka takura min ka bar Ni in yi rayuwata cikin salama, idan ba Ni na kira ka ba don't call me again please." Daga haka ta katse kiran ɗib Wani irin baƙin ciki ne ya turniƙe zuciyar SHAREEF wanda ya kasa kataɓus a wurin, sai ga hawaye sharr suna fitowa daga cikin idanuwansa wanda ya kasa tsayar dasu, ƙanƙame zanin gadon yayi zuciyarsa na tafarfasa kamar zata ƙone don takaici, yau wai shi Haseena take wulaƙanta wa? Shi SHAREEF Haseena take wulaƙanta wa take faɗa masa waɗannan munanan maganganun? Tabbas a yau yana dana-sanin sanin ta a rayuwarsa, ashe duk soyayyar da suke yi wa juna wata rana zata iya juya masa baya? Abun takaicin yanda yake jin soyayyarta na ƙara ninkuwa a cikin zuciyarsa, baƙin cikin yayi masa yawa ji yake yi kamar yayi hauka don takaici, ya kasa tsayar da ruwan hawayensa sabida hakan ne kawai zai sa ya samu salama, da yana da halin da zai cire ta a rai babu abun da zai hana shi aiwatar wa a yau, ya barta har abada koda ita ce Autan Mata, wlh yayi nadamar sanin ta sosai, Maganganun Momy ne suka ƙara rikirkitar dashi hankalinsa yana ƙara tashi ya rasa mai ke masa daɗi a duniya A haka Hanif ya zo ya tarar dashi cikin wannan halin yana hawaye kashirɓan, ba ƙaramin tayar masa da hankali yayi ba sabida rabon da ya ga ɗan uwansa a wannan mugun yanayin ya jima, musamman yanda yake kwararar da hawaye mai yawa har haka, Cikin tashin hankali ya matsa kusa dashi yana tambayarsa ba'asin kukan nasa? Yayinda zuciyar SHAREEF na tafarfasa yake duban Hanif ɗin, idanunsa sun yi ja sun kumbura suntum ga damuwa da ke tattare a kan face ɗin sa, yayinda cikin sanyi da karayar zuciya yake cewa, "ban san me nayi Allah ke jarabta na da soyayyar Haseena ba, na kasa cire ta a raina kamar yanda itama yanzu ta dena so na, Haseena ta sauya min ta dena son farin cikina, ban taɓa tunanin zata juya min baya ba, amma kullum jin sonta nake yi har cikin raina." Sai ya ja numfashi daƙyar ya ƙara da faɗin, "ina son in manta da ita a raina amma ban san yanda zan yi ba, kamar Ni SHAREEF har na kai lalacewar da wata Mace zata iya wulaƙanta Ni?" Girgiza kansa Hanif yayi cike da tausayinsa, don ba ƙaramin tausaya mishi yayi ba sabida ya san cewa tabbas yana cikin wani hali da ciwon abun, but sai yace, "Mace ta wuce tunanin ka Bro, duk yanda ka so da nuna mata kai ne a saman ta; gata da nasaba da kyawu gami da tsantsan wayewa; a wurin Mace ba komai bane kai Bro, musamman idan akwai soyayya. Ba tun yau ba na ce maka ka cire yarinyar nan a ranka ka ƙi, already yanzu ba sonka take yi ba, why not baza ka iya ɓanɓare ta a rayuwarka ba? Ba fa ita kaɗai bace Mace a duniya ba, sai lokacin da ta kaika ta baro zaka san cewa kana aikata kuskure. Duk abubuwan da kake ji haka itama Maryam ta ji sa a baya, amma ka kasa tausaya mata, ka rufe idanuwanka ka wulaƙanta ta batare da tausayi ko rangwanta mata a matsayin ta na yarinya ƙarama ba, ka kasa fahimtar zuciyarta da Allah ya ɗaura mata ciwon son ka, tayi haukan tayi kukan duk don soyayyar da take maka, ta juri kowacce wulaƙanci naka; amma...." Sai yayi shiru yana jan numfashi tare da kallon fuskar SHAREEF ɗin, sai ya kaɗa kansa da cewan, "i know har da alhakin ta Bro, a tunanina Allah ya ɗaura maka don kaima ka ɗanɗana abun da wasu suke ji in aka kasa tausaya musu don sun faɗa irin wannan ƙaddaran; wanda basu suke ɗaurawa kansu ba, don Allah ko ya ya ne ka saka wa kanka tausayin mutane SHAREEF, ka damu da damuwar waɗanda suka damu da kai." Shiru SHAREEF yayi ya kasa magana, domin ba ƙaramin ɗaure sa da jijiyoyin jikinsa yayi ba, wanda yasa ko idanunsa ya kasa ɗagowa bare ya kalle sa ko ya furta abun da ke ransa Sai Hanif ɗin ya dafa mishi kafaɗa gami da faɗin, "shawaran da zan baka a matsayina na ɗan uwanka; kuma in CeCe ka a wannan halin da kake ciki; na farko shine addu'a, ka roƙi Allah ya cire maka soyayyar Haseena, domin baza ka taɓa samun wannan farin cikin da kake biɗa a wurin ta ba, sannan..." Sai yayi shiru yana tunanin ta inda zai faɗa mishi abun da ke ransa, Haka nan ya daure ya ci gaba da maganar, "duk da na san ba ka ƙaunar Maryam, amma har yanzu ita Matarka ce, na san a ranka kana wannan saƙar da baza ka taɓa zuwa wurin ta ka nemi buƙata ba, shiyasa kake zaune cikin wannan halin, Ni zan taimaka maka." Haɗa idanu suka yi da SHAREEF ɗin, sai yayi mishi murmushi da ɗaga kai tare da sake faɗin, "akwai wani shawara, mai zai hana ka neme ta batare da sanin ta ba. I mean koda maganin barci ne ka sanya mata hakan zai taimaka maka ka fita a wannan halin da kake ciki, Ni ɗan uwanka ne bazan so abun da zai cutar da kai ba, i will help you a kowanne hali kake ciki. This is the best solution we have". [13/04, 7:34 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE18* _____Abun mamakin sam SHAREEF bai musa daga shawarar da Hanif ya ba shi ba, domin a ganin sa wannan hanyar ne kaɗai ya rage mishi wajen samun sauƙi daga damuwar da yake ciki, sannan ma da biyu ya amince; ko don ya koya wa Maryamu hankali ya hukunta ta, dama ai ta taɓa mishi sharri makamancin haka, yanzu zai tabbatar mata da gaskiyar al'amarin, lallai bata san waye shi ba Yayinda Hanif ya ji daɗin yanda SHAREEF ya fahimce sa; domin bai taɓa tunanin hakan ba ko don furucin sa na baya, shi kuma a ganinsa hanya ce mai sauƙi da SHAREEF zai soma son Maryamu tunda har irin wannan abun mai girma zai shiga tsakanin su, tabbas yanzu an samu sauyi tunda har ya amince zai iya kusantan Maryamu, lallai Kura tayi lafiya, to abu mai sauƙi ne ya kamu da soyayyarta, ya ji dad'i sosai, Shiyasa yace mishi, "zuwa gobe sai su siya maganin barci su saka mata, ya san plan ɗin da zai yi har ta sha." Da haka suka bar zancen, amma sam SHAREEF ya kasa runtsawa a wannan daren, abu biyu ke damunsa, yanda Haseena ta juya masa baya; da kuma surar Maryamu da ke mishi gizau yana ƙara jin kwaɗayin kasancewa da ita. in takaice muku har mafarkin ta SHAREEF yayi a wannan ranan, sabida ya sa abun a ransa, Allah -Allah yake yi goben yayi ya gansa tare da ita yana biya wa kansa buƙata ko zai samu sukuni daga gangan jikinsa A washe gari haka suka wuce Office tare da Hanif, yau ma sai da ya biya ta hospital aka yi mishi ƙarison alluran nasa, tare da Hanif suka je sannan suka wuce wurin aiki After sun tashi wurin ƙarfe biyar da rabi, don yau sun jima a companin sabida wasu ƴan gyare-gyare da ake yi, ga meeting da suka yi a ƙurarren lokaci, dalilin da yasa suka kai wannan lokacin kenan A hanya da zasu dawo Hanif ya faɗa masa, "zai tsaya su siya yoghurt, sabida a ciki za a sanya mata maganin barcin, shi zai san yanda zai yi ta sha Insha Allahu." Bayan sun tsaya sun siya, suka ƙarisa wani Pharmacy suka siya maganin sannan suka wuce gida Har a ran SHAREEF wani dad'i yake bijiro masa ya rasa daga ina yake jin wannan farin cikin, abun da zai iya cewa kawai don yau zai kawar da kwaɗayin sa ne, shiyasa maybe yake jin farin ciki a ƙasan zuciyarsa, tunda sam bai damu da Maryamu ba sannan ba ya jin ta a rai kamar yanda yake kwaɗayin jikinta, gaskiya tana da dirin da babu ƙarya ta saka shi a wani yanayi, bai taɓa tunanin haka yarinyar take da kyakkyawar sura ba, ko kuma don ta ƙara girma ne? Haka yake ta tunani a ransa yana son ya ƙara tozali da ita, Amma koda suka koma bai same ta a gida ba, sai baza idanu yake yi ko zai ganta, in fact ma a falon ya zauna koda suka dawo yana son ya ga gibtawar ta, amma bai ganta ba, kuma babu damar tambaya Yayinda Maryamu kuwa yau a gidan su Feena ta wuni, takai mata ziyara, tunda tun dawowarta Hutu bata je ba, su kansu basu san ta dawo nan Hutu ba, sai yau da ta je tayi mata wuni, daga nan suka tafi gidan su Amina a tare Sai yanzu ne Momy ta aiki Sadiq ya je ya dauko ta, lokacin ya fita kenan su SHAREEF suka dawo gidan Sai bayan magriba suka shigo shi da Maryamun, Dayake suna shiga aka kira sallan isha'i that's why Sadiq ya wuce masjid, itama Maryamu ta shiga dakinta ta gabatar da Sallah, bayan ta idar ta shiga tayi wanka sannan ta shirya cikin doguwar rigan material mai sauƙin nauyi kalan dack brown da design ɗin flowers masu kalan ja, rigan A. Shape ne mai aljihu da dogon hannu an sanya robber a ƙarshen, sai ta saka hula a kanta ta rufe tulin gashinta, takalmi kawai ta zura ta fita Falon suka zauna da Momy suna kallo, while tana bama Momy labarin fitan da tayi tunda ta tambaye ta Sai da aka idar da Sallah sannan su Dady suka shigo gidan gaba ɗaya, Sai lokacin SHAREEF ya hangi Maryamu idanunsa a kanta ya kasa ɗauke kai yana sake ƙare mata kallo, a ransa har ya hango abun da zai wakana a tsakanin su Ko kusa bata kalli inda yake ba balle ta nuna Allah yayi ruwan tsakin sa a wurin, harkan gabanta kawai take yi, bata san ma sanda ya bar wurin ya wuce ɗaki yin wanka ba, Suna zaune da su Hanif suna hira sai dariya suke yi, Sai daga baya ne suka tashi suka ci abinci a saman dining, after sun gama suka dawo Falo suna ɗan taɓa hira, Tun lokacin Maryamu ta soma jin barci tunda ba ta jimirin jima wa yin hira, in har ka ga ta tsaya hira to ta sha barci da rana ne, wanda kuma hakan ba sabon ta bane zai yi wuya Maryamu tayi barcin rana in har lafiyarta ƙalau, Suna cikin duba waya ita da Sadiq, yana nuna mata wasu abubuwan da bata gane ba a sabuwar wayanta, Har ta soma gyangyaɗi sai kuma tace mishi, "ya bari zuwa gobe sai su ci gaba." Bayan ya bata wayan tayi musu sallama ta wuce ɗaki Momy na sake gargaɗan ta, "kar ta kwanta bata yi addu'a ba." Domin koyaushe sai ta tuna mata in har zata tafi daki sai ta sake gargaɗin ta Ta amsa mata da, "to." Tana wucewa Hanif ganin ta tafi shima sai yayi musu sallama ya wuce, Yana zuwa ɗakin su ya ga SHAREEF har yayi wanka ya zura jallabiya a jikinsa, yana zaune a bakin gadon yana jiran sa, sai ga shi ya shigo da sauri yana dariya da faɗin, "Bro mutumiyar taka fa ta shige ɗaki zata kwanta, bari in kai mata yoghurt ɗin kar barci ya kwashe ta." Kansa ya gyaɗa masa a hankali yana kallonsa batare da ya ce komai ba, Har sai da ya fice before ya mayar da idanuwansa ya rufe yana jan numfashi, shi kaɗai ya san halin da yake ciki yanzu, sai faman cije laɓɓa yake yi yana tsimayin jiran Hanif While Hanif kuma dama yoghurt ɗin a Falonsu ya ajiye cikin fridge, ɗauka yayi ya fita ta benen baya wanda zai sada mutum da corridorn ɗakin da Maryamu take, batare da wanda yake zaune a falo ya ga gilmawan sa ba, Tura ƙofan yayi a hankali ya ji ta buɗe, bai shiga ba sai da yayi sallama yana kiran sunanta Hakan ne yasa Maryamu da ke kwance ta rufe kanta a cikin blanket, tsaban barci ne a idanuwanta tana shiga ta faɗa kan gadon, har barci ya soma tafiya da ita ta ji sallaman sa kamar a sama, bata tantance waye ba amma ta buɗe idanuwanta tayi shiru tana sauraron wanda zai shigo Shi kuma Hanif bai shiga ba sai da ya ƙara yin sallama jin shiru, tare da kiran sunan ta yana cewa, "My sister, kin yi barci ne?" Ta gane muryan waye, dalilin da yasa ta mike zaune tana cewa, "A'a Yaya Hanif, ka shigo." Ƙarisa tura ƙofan yayi ya shige cikin ɗakin, ganin akwai duhu sai ya kunna fitilan ɗakin da makunnin yake bakin ƙofan, Fuskarsa da murmushi yake kallonta yace, "har kin yi barci kenan? Na tashe ki ko?" "A'a Yaya, ban fara ba ma." Wurin ta ya nufa yana faɗin, "na manta ɗazu ban ba ki yoghurt din nan da na siyo miki ba, sai da na shiga ɗaki na gani shiyasa nace bari in kawo miki." Hannu ta saka ta amsa cike da farin ciki tace, "Wow! Yayana kamar ka san ina son yoghurt wlh, musamman ma wannan Rufaidan, dama ban taɓa sha ba ina ta son in ɗanɗana." Dariya yayi sabida ganin yanda take santi har ta buɗe zata sha, sai da ya ga ta kafa kai ta soma sha sannan yace, "ai komai kike so my sister zan yi miki, don haka daga yau ma zan riƙa siyo miki tunda na ga kina so, bari in je kar in takura miki, good night." "Ok Yaya, Nagode Allah ya saka da alkhairi, sai da safe." Tayi maganar bayan ta cire robbern a bakinta tana kallonsa Murmushi yayi mata kawai ya fice cike da jin daɗin ta sha, da sauri ya koma ɗakin su ya samu SHAREEF ya fito Falo yana tsaye sai faman zirga-zirga yake yi, "Yauwa My Bro, komai fa ya kammala, don yanzu haka sai da ta sha sannan na fito daga ɗakin." Dariya ya ƙara yi yace, "amma fa ka kula kar ka je kayi abun da ba daidai ba, har yanzu Maryamu yarinya ce baza ta ɗauki wannan jaraban naka da ka jima kana neman inda zaka sauke ta ba." Wani kallo SHAREEF ya watsa mishi, sai ya ja dogon tsaki yana wuce wa zai fice batare da ya ce uffan ba Yayinda Hanif kuwa dariya kawai yake yi har sai da ya ga fitan sa, kana shima ya wuce bedroom yana ɗaukar wayansa ya hau rubuta wa Amra saƙo ransa fari ƙal, domin bai da farin cikin da ya wuce ta sanadin haka SHAREEF ya soma ƙaunar Maryamu, har ransa yana son su kasance tare domin sun dace, amma SHAREEF ya kasa gane wa taurin kai da bahagon zuciyarsa ya kasa sanin fari bare baƙi. *** Tun fitan Hanif sai Maryamu ta ajiye yoghurt ɗin bata ƙara sha ba, dama ba wani sha sosai tayi ba sabida barcin da ke rufe mata ido, ajiye wa tayi da ninyar gobe ta shanye, sai ta gyara kwanciyarta ta shige cikin blanket, nan da nan barci mai daɗi ya sure ta cikin ƙanƙanin lokaci ko kashe fitilan bata yi ba Yayinda SHAREEF a dai-dai wannan lokacin yana bakin ƙofan ta ya jima yana tsaye, yana son tayi nisa a barcin nata sannan ya shiga, sai da ya ɓata lokaci before ya murɗa handle din a hankali ya zura kansa ciki, ganin ta a kwance ba ta motsi; hakan ne yasa ya ɗan saki ajiyar zuciya, before ya ƙarisa zura ƙafafunsa ya shige gaba ɗaya, a hankali ya mayar da ƙofan ya rufe, Tsayuwa yayi a wurin yana kallon inda take, duk da ba ya ganin komai nata domin har kanta ta shigar ta rufe, Kusan mintina biyu before ya saka hannu ya kashe hasken ɗakin, sannan a hankali ya taka zuwa bakin gadon ya sake tsayawa, Ya jima a tsaye yana tunanin ta inda zai fara, sai da yayi ƙuru kamar ya juya amma sai ya daure ya haye saman gadon a hankali yake moving har ya shige cikin blanket ɗin, tare da janyo ta jikinsa ya ƙanƙame ta yana sauke ajiyar zuciya sabida wani irin natsuwa da ya saukar masa, jikinsa har rawa yake yi wurin ƙoƙarinsa na aiwatar da abun da yake ninyar yi, lokaci ɗaya ya rikice sabida jin albarkatun jikinta ya haɗe da nashi, musamman yanda ya ji ɗumin jikinta ya soma ratsa shi, nan take wani irin sha'awa mai ƙarfi ya taso masa, gaba ɗaya ya soma susuce wa ya soma fita a hayyacinsa koda ganin yanda yake yamutsa ta cikin zafin nama da rashin natsuwa Yayinda Maryamu bata san me yake wakana ba a wannan lokacin, domin ba karamin nisa tayi a barcin ta ba, duk bidirin da SHAREEF yake yi wurin romancing ɗin ta tamkar zai cinye ta, har da cire mata riga; bata san mai yake wakana ba sai da abu yayi nisa yana ƙoƙarin afka mata da karfi da yaji, a lokacin ne tayi firgigit ta tashi a tsorace tana zazzare ido, lokaci guda kuma ta saka ƙara sabida tunanin ta wani ne ya shigo ɗakin, ihu take yi kamar zautacciya tana son ƙwace jikinta tare da ɓanɓare shi a jikinta; yanda ya nane mata ya kifa kansa saman ƙirjinta yana lashe ta abun ya bata tsoro, dalilin da yasa ta dinga tsala ihu kenan tana janyo mishi gashin kansa da hannunta ya sauka a kai Wanda hakan ne yasa SHAREEF ya soma dawowa cikin hayyacinsa, bai ida nufin sa ba ya ɗago yana duban ta daga cikin hasken farin watan da ya ƙillaro a ɗakin, ya kasa magana sai jan numfashi yake yi yana duban ta, bazai iya biye mata ba abun da yake buri kawai ya samu biyan buƙata, shiyasa nan take yayi kokarin ci gaba da abun da yake yi, amma kukanta da ihun ta ya soma firgitar dashi gudun ta jawo mishi mutane, da sauri ya sanya hannu ya rufe mata bakin yana faɗin, "shiiii! Ni ne, ki natsu Malama kar ki jawo min mutane nan." Gabanta ne yayi wani irin bugawa jin muryan SHAREEF ya ratsa mata kunnuwa, take ta dawo hayyacinta ta dena bige-bigen da take yi tana son gasgata mafarkin da ta saba yi ne a baya; yanzu yake faruwa da ita ko kuma shi ne da gasken? Ganin ya ci gaba da lashe ta kamar tsohon maye take ta sanya ƙarfin ta da hannayenta biyu tana shirin ɓanɓare shi; bakin ta ɗauke da salati sabida har lokacin bata yarda cewan SHAREEF ne a gaske ba, Hannu ta sa ta ja gashin sa dole ya dakata da abun da yake yi yana janye jikinsa tare da faɗa wa gefenta; jikinsa rabi a jikinta yana jan numfashi, Ita kuma hakan ne ya bata damar ƙwace jikinta ta faɗo daga kan gadon, jiki na rawa ta miƙe tana neman hanyar fita sabida ruɗewan da tayi Da sauri SHAREEF ya mike ya cafko ta ya riƙe ta gam yana cewa, "kee! Wlh kika tara min mutane sai na ci ubanki, baza ki natsu ba?" Amma inaa; sam ba ta jin sa illa fasa kuka da tayi tana son fincike wa ta gudu, kamo ta yayi ya dawo da ita kan gadon ya jefa ta a fusace yana cewa, "don ubanki baza ki yi min shiru ba sai kin tara min jama'a? Abun da kike nema ne na zo muyi tunda kin iya sharri, yanzu sai ki samu damar yin sharrin da kyau in nayi miki zahiri kika gani. Shashasha idan ma ba lalura ba mai zai sa in kawo kaina wurin ki?" Kuka Maryamu take yi ta kasa ma sauraron sa; ƙoƙarin ta kawai tabar ɗakin domin har yanzu gani take yi mafarkin da ta saba yi a baya ne; ba gaske ne ba, sosai take ɓarin baki tana addu'o'i a cikin zuciyarta, Can ta hantsala ta takure a jikin bango tana ci gaba da kuka mai fita da ƙarfin sauti Takaici ya cika SHAREEF sabida rashin biyan buƙata, ga shi a ƙage yake gaba ɗaya ƙarfin sa ya ƙare mugun kasala da tsananin sha'awa ke addabar sa, hakan ne yasa ya kasa jurewa ya nufe ta gadan-gadan zai afka mata Amma tuni ta zille ta sake wantsala wa ta inda ya baro, Sai abun ya zame musu kamar wasan Yara, Idan yayi nan tayi can tana kuka da ƙarfi a kokarinta ta samu ta fice, Amma ya tare mata hanya idan ta nufi ƙofan zai iya kama ta, shiyasa take hawa saman gadon tana ƙara volume ɗin kukan ta har yanzu bata yarda SHAREEF ne zahiri ya zo gare ta ba, addu'a fal bakin ta wadda gaba ɗaya halin ruɗewa da tsantsan tsoro; yasa ba ta iya gane abun da take furta wa, A fili take karanto addu'o'in nata har da su wa'innahu Sulaimau... Da gudun ta ta dumfari toilet ɗin cikin dakin ta shige zuruf har tana gwara kanta da bango, amma inaa; bata saurarawa kanta ba duk da azaban da ya ratsa ta, fatan ta kawai ta samu ta shige domin ta tsira, Tana shiga ta mayar da ƙofan zata datse Amma kafin ta rufe ɗin ne SHAREEF ya kaima ƙofan bugu kamar wani mayunwacin Zaki Lokaci ɗaya ƙofan ta buga kan Maryamu ta watse a ƙasa; tana ƙwallara ƙara mai firgitar wa. [15/04, 7:16 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE19* _____Shi kansa ya tsorata ganin yanda ta zube a ƙasa tana ihu ya buga mata kai, Da sauri ya duƙa a ƙasan yana kamo ta yayi saurin rufe mata baki don ya samu ta dena ihun, gam ya rufe mata bakin tana ƙoƙarin ƙwace wa duk da jigatan da tayi but burinta kawai ta ƙwace tayi ta kanta, Amma SHAREEF ya hana wannan damar, da sauri yayi ƙoƙarin ɗaukar ta zai mayar da ita saman gadon da zafin namansa Maryamu jikinta na rawa ta fincike don a yanzu ta soma gane SHAREEF ne ba mafarki ba, Ganin da ƙarfin yana son tafiya da ita shiyasa ta gantsara mishi cizo; nan take ya sake ta, ta ja baya tana sauke nimfarfashi kamar wacce zata mutu sai haki take yi, Sai kuma tayi saurin kare ƙirjinta sabida babu riga a jikinta tuni ya cire mata, kuka ta fasa mishi tana faɗin, "meye ya kawo ka wurina? Me zaka yi min?" SHAREEF da ke duba hannunsa azaba ya ishe sa, ransa yayi mugun ɓaci shiyasa ya miƙe da iya ƙarfin sa ya ɗauke ta duk da wutsil-wutsil ɗin da take yi, a kan gado ya jefa ta da ƙarfi cikin mugunta ya bi kanta zai faɗa, Amma sai tayi saurin goce wa zata sake sauka, Kamo ta yayi ya falla mata mari mai firgitar wa Azaban da ya ratsa ta sai da tayi suman wucin gadi before ta dawo hayyacinta, wani irin marayan kuka ta fashe dashi tana ƙanƙame jikinta sosai; wanda ta kasa ba shi damar ci gaba da taɓa ta, yana kawo hannunsa jikinta a haukace takai mishi mamaya kamar Kura ta gantsara mishi wani cizon ta ƙi sakin hannun, gaba ɗaya ta haukace mishi yana fizgewa tana kai mishi mamaya ta ko'ina da ninyar duk inda ta samu ta farfasa mishi da haƙoranta SHAREEF sosai ya tsorata hankalinsa ya tashi, nan take ya miƙe yayi nasaran janye jikinsa, baƙin ciki da takaicin ta yasa ya ƙara maka mata wani marin, ransa a ɓace yace, "ke don ubanki Ni kike cizo don uwarki?" Ɗago jajayen idanuwanta tayi ta zuba mishi tana sauke haki, daƙyar take iya faɗin, "mugu azzalumi kwarto kawai, ba dai Uwana ba wlh, kuma ka fitan min a ɗaki ko in je in sanar da su Dady, wlh baza ka taɓa samun abun da kake so ba tunda..." Bata sauke maganar nata ba ya ƙara kwashe ta da marin da sai da ta kama kumatun nata ta tsandara uban kuka tana kiran sunan Innan ta Hannu yasa a wuyanta ya shaƙo ta kamar zai cire mata rai don tsaban fushin da yayi, sam ba shi a cikin hayyacinsa sabida zagin da tayi masa, "Idan kika sake yunkurin zagina makamancin haka, sai na illata ki na kashe ki, don ubanki mai kike dashi da zan zo wurin ki kina wulaƙanta Ni? Na fi ƙarfin wulaƙanci bare a wurin ki ƴar ƙauye Bagidajiyar banza." Sai ya ja mata breast ɗaya da iya ƙarfin sa na mugunta, "a kan wannan banzan abun kike son zagina ko? To ki riƙe ki cinye, shegiya muna-fuka mai bak'ar fuska." Sai ya sa hannu ya ture ta ya rarumi rigansa ya fice ko gyara wandon sa da ke ƙoƙarin kayar dashi bai yi ba; tunda a zame yake yana ƙoƙarin fice wa daga jikinsa Ya kasa ƙarisa wa cikin dakin su, sai ma zama a falon ƙasa yayi yana sauke ajiyar zuciya gaba ɗaya ransa ya jagule da ɓacin ran da Maryamu ta sanya shi, zuciyarsa tafarfasa take yi tun farko maiyasa ya biye wa Hanif har ya aikata wannan banzan abun; da yarinya zata raina shi? shikenan yanzu ya ja wa kansa raini a banza a hofi ya je ya nemi buƙata a wurin yarinyar da yake ganin ba komai ba, Yanda maƙogwaron sa ya bushe yana jin kamar numfashinsa zai bar gangar jikinsa, hakan ne yasa da sauri ya mike ya nufi wurin fridge ya dauki ruwa ya soma sha kamar zai saka goran a cikin sa, don sai da goran ta lotse sabida yanda yake zuƙo ruwan, cikin ƙanƙanin lokaci ya shanye ruwan Faron yana jefar da goran, Ajiyar zuciya ya dinga sauke wa a kai- a kai ransa yana ƙara ɓaci, har yanzu ya kasa samun sukuni daga raɗaɗin da yake ji, Wandon sa ya gyara sannan ya mayar da rigan ya nufi ɗakin su Abun mamakin koda ya shiga ya samu Hanif na zaune a falon su ya ɗaura kafafu a saman Centre table yana ta faman latsa waya, Shi kansa ya tsorata ganin yanda SHAREEF ya banko ƙofan ya shigo, da sauri ya dube sa ya ga yanda ya haɗa gumi idanunsa sun kaɗa sun yi jawur, sai tsuma yake yi jijiyoyin wuyansa sun fito raɗo-raɗo, hankalin sa ya tashi nan da nan ya soma tambayarsa, tuni ya miƙe a kan ƙafafunsa yana duban sa Zama SHAREEF yayi yana kama kansa wanda kamar zai cire don bala'in ciwon da ya kamo mishi mamaya, yanda ransa a ɓace bazai iya buɗe baki yayi magana ba, shiyasa yayi shiru yana jin yanda Hanif ke ta faman jero mishi tambayoyi amma ya kasa amsa ko daya, Sai da ya dame sa sannan ya ɗago a fusace yace, "kwanyan ka ta faɗa yarinya ta samu damar da zata raina Ni, har ita wace ce da zan je da buƙata ta wurin ta ta wulakanta Ni? Ni na fi ƙarfin wulaƙanci wlh, idan na jure na Haseena bazan taɓa jure na wannan banziyar yarinyar ƙasƙantacciya ba, Jahilar yarinya mara ilmi, wlh kaɗan ma nayi mata, ba don kar su Momy su ɗauki fushi da Ni ba da sai na taye mata gaba ɗaya bak'ar fuskar nan nata, Jakar yarinya kawai..." "Haba Bro enough mana don Allah, ya za a yi ka tasa yarinya kana zagi haka kawai don son zuciya irin naka? Kar dai a ce dukan ta kayi kuma daga zuwa cin arziki?" "Kashe ta nayi, ko zaka rama mata ne? Ban ga yarinyar da ta isa in zauna ina biye mata ba, wlh ka cuce Ni Hanif, amma zan ɗauki mummunan mataki a kanta tunda so take yi ta raina Ni, har Ni zan zage ta ta rama?" Cike da takaicin sa Hanif yake kallonsa, abun ma ya ɗaure masa kai ganin yanda yake faɗa yana tayar da jijiyoyin wuya, sai da ya gama tsab before yace, "let me told you abun da baka sani ba SHAREEF, Maryam ta fi Haseena sau dubu a wurin ka." Ganin yanda SHAREEF ɗin yayi masa wani kallo kamar zai shaƙo sa, sai shima ya ware mishi nashi idanun yana ƙara wa da faɗin, "Yes of course, abin da baka sani bane zan faɗa maka yanzu ko don ka gane Maryam ba abun wulaƙanci bane a wurin ka, har yau baka san wace ce ita a gare ka ba, meyasa kake son sai ka wulaƙanta ta ne? Meyasa ka kasa gane soyayyar da Maryam take maka ne? Bari in faɗa maka abun da baka sani ba, ita wannan da kake zagi a kullum kake ganin ta a ƙasƙance; ita ce ta sadaukar da rayuwarta da lafiyarta domin ta ga naka lafiyar ya inganta, idan baka sani ba Maryam ita ta baka ƙodan ta aka saka maka har a yanzu kake ci gaba da rayuwa kake wulaƙanta ta, kake ganin kamar jahila ce bata san mai take yi ba, amma soyayyar da take maka har ta iya sadaukar da wani ɓangare na jikinta domin ta taimake ka, haba Bro idan baka so ta ka tausaya mata ba; wa zaka yi wa?" Da sakakken baki SHAREEF yake bin sa da kallo, cikin tsananin mamakin furucin sa yace, "kana nufin ita ta bani ƙoda aka saka min?" Tashi Hanif yayi fuskarsa a ɗaure yake duban sa a yanzu, "Yes ita ta baka, Ni kaina ban sani ba sai kwanaki da Sadiq yake bani labari, abun ya ɗaure min kai, shin maiyasa su Momy suka yarda har aka cire mata ƙoda aka saka maka bayan sun san ba ka sonta ba ka ƙaunarta? Mene ne dalilin ɓoye maka da suka kasa faɗa maka ko don ka dawo hayyacinka ka san cewa Maryam ba abun tozarci a gare ka bane." Sai ya jinjina kansa yana ƙara wa da faɗin, "don Allah Bro ka sauya hali, amma..." Sai yayi shiru sabida ransa yayi mugun ɓaci, in yace zai ci gaba da magana zai gaya masa maganganun da zasu ɓata mishi rai ne, sam SHAREEF bai da kirki wlh, wuce wa kawai yayi yabar sa a wurin Yayinda SHAREEF ya kasa motsi a wajen kamar an dasa shi, maganganun Hanif suna ƙara mishi ƙuwa a cikin kunne. *** A yanda yabar Maryamu, a haka ta ƙudundune kanta ta dinga sharɓan kuka gunun tausayi, ga raɗaɗin marukan da ya sauke mata har yanzu tana jin ƙaran marin a cikin kunnenta, kuka sosai ta dinga yi ta kasa sararawa kanta sabida tsananin baƙin cikin abun da SHAREEF yayi mata, lokaci ɗaya ta soma jin tsanarsa na huda mata can cikin zuciya baƙin ciki da ƙunci suka tokare mata maƙogwaro, A haka ta kwana cikin wannan halin ko motsa wa ta kasa yi illa hawaye da take zubar wa cuz sautin muryanta ma ya dena fita, ba ƙaramin jigata tayi ba sabida wani irin ciwon kai da ya cafke ta, Har aka yi kiran sallan asuba a kunnenta aka yi tana ƙudundune da kanta a saman cinyanta ta cure wuri ɗaya ta kasa motsa wa, Dalilin da yasa koda ta miƙe zata shiga toilet jikinta yayi tsami wuyanta ya riƙe ƙam daƙyar take iya sarrafa kanta, idanun nan sun kaɗa sun yi jazur haka ma fuskarta tayi suntum, a haka ta lallaɓa tayi sallan a zaune sannan ta kwanta a wurin tana mayar da nimfashi, sai tsiyayar da hawaye take yi waɗanda sun kasa tsaya wa daga cikin idanuwanta, a duk shuɗewar seconni tana jin ƙiyayyar SHAREEF na ƙara huda mata zuciya, haƙiƙa tayi nadamar sanin sa, a yanzu dai baza ta taɓa iya auren mugu azzalumi mara imani irin sa ba, wlh sai dai ta mutu da ta zauna dashi koda soyayyarsa zai kashe ta ne, bare ma a yanzu jin ƙiyayyarsa take yi, A nan ta kwanta ta kasa motsi har garin Allah ya waye lokaci ya soma ƙurewa amma ta ƙi tashi, Sai da kusan ƙarfe tara tayi sannan ta miƙe zaune daƙyar, ba ta son Momy ta zo ta tarar da ita a haka shiyasa ta lallaɓa ta shiga toilet tayi wanka, ta fito ta zauna a bakin dressing mirror tana kallon fuskarta, daga ita sai towel da ta ɗaura daga saman ƙirjinta har zuwa cinyoyinta, ido ta tsira wa madubin tana jin wasu zafafan hawaye suna ƙoƙarin fitowa, sabida ganin yadda face ɗin ta tayi mugun kumbura sakamakon marin da ta sha; da kuma kwana da tayi tana kuka ga rashin barci, babu shatin yatsu amma duk kumatun ta sun suntume, manyan idanuwanta sun yo waje sun kumbura ciki sun yi jazur alamun ta sha kuka sosai, har saman laɓɓanta sai da suka tasa, Wani irin kuka ta fashe dashi tana kai hannunta ɗaya zuwa saman bakin ta, cikin shashsheƙan kuka take faɗin, "Allah ya isa ban yafe ba, Insha Allahu Allah sai ya rama min abun da kayi min, bazan taɓa yafe maka ba." Ɗakyar ta iya tsayar da kukan ta tashi ta je ta sanya riga da wando na fakistan, sannan ta yafa mayafi a saman kanta ta fita Falo Babu kowa sai Momy wacce itama tana shirin kiran Maryamun ne da ta ji ta shiru, amma ganin ta a wannan yanayin fuska ta kumbura, hankalinta a tashe take dubanta da tambayar ta, "me ya same ta?" Ɗakyar Maryamu ta mayar da ƙwallan da ke shirin zubo mata, tace, "Momy babu komai." "Ya za a yi ki ce min babu komai; bayan ji be yadda kika fito fuska a kumbure alamun kin sha kuka? Sanar min mai ke damun ki?" "Momy ciwon kai ne jiya ya dame Ni shine na kasa barci." "Subhanallah.. amma ai yakamata ki zo ki tashe Ni in ba ki magani Maryam, ba wai ki zauna kina kuka ki bar ciwo a jikinki ba, ko da asuba maimakon ki taso ki zo in ba ki maganin, kar ki ƙara haka kinji ko? Bari in kawo miki maganin, ki je ki zauna ki karya ina zuwa." Tayi maganar tana tashi ta nufi upstairs da sauri domin ɗauko mata maganin Yayinda Maryamu kuma ta ƙarisa wurin dinning ɗin ta zauna, sai da tayi shiru na tsawon lokaci before ta soma haɗa tea a hankali cikin sanyin jiki da rashin karsashi, har ta gama before Momy ta kawo mata maganin, Hakan ne yasa ta afa a baki ta sha da tea ɗin Momy kuma ta ƙarisa zuba mata arish da ƙwai a flat, ta ɗaura mata bread a sama before ta tura mata gabanta, tana ce mata, "tayi maza-maza ta ci." Falo ta koma ta zauna tana duba wayanta tana son tayi kira A time ɗin SHAREEF shima ya fito, domin shi kansa bai samu yayi ishashshen barci ba sakamakon abun da Hanif ya faɗa masa a jiya, sosai maganar ta tsaya mishi a rai cike da tsananin mamakin wai Maryamu ne ta ba shi ƙodan ta, tsananin takaici da dana-sanin abun da yayi mata ne ya kasa runtsa wa sai gab da asuba barci ɓarawo ya kwashe sa, Har garin Allah yayi bai tashi ba Yayinda Hanif yayi shirin zuwa aikin sa ya tsallake sa ya wuce batare da ya tashe shi ba, ya wuce wurin aiki shi kaɗai Sai yanzu SHAREEF ya farka ya ga ya makara, wanka yayi ya ɗaura alwala yayi Sallah ya shirya sannan ya fito riƙe da Jakarsa, Tun dosowan sa Falon ya hangi Maryamu zaune a saman dinning, kanta a ƙasa tana kallon cikin cup ɗin da ke gabanta ta kasa shanye wa sabida halin da take ciki na rashin daɗin jiki; da kuma ƙuncin zuciya, A hankali ya taka ya iso cikin Falon yana ma Momy Barka da safiya Ta dube sa tace, "sai yanzu? Ai nayi tunanin baza ka je aikin bane ga shi har ƙarfe tara da rabi, Hanif ya daɗe da tafiya." Shiru yayi bai ce komai ba kuma bai zauna ba Itama sai ta mayar da hankalin ta a kan wayanta tana cewa, "ka je ka karya." Juya wa yayi bai ce uffan ba ya nufi wurin dinning ɗin, har ya ƙarisa idanunsa a kan Maryamu da ta ƙi ɗagowa kanta a ƙasa ba ya ganin fuskarta, tsaya wa yayi a wurin ya zuba mata ido yana jin zuciyarsa babu dad'i, musamman lokacin da ta ɗago kanta tana shirin mike wa tabar wurin, hakan ne yasa ya ga fuskarta wacce take a kumbure babu ɓurɓushin fara'a, tana barin wurin sai ya lumshe idanunsa, a karon farko a rayuwarsa, a karon farko ya ji tausayinta da kuma tsananin nadamar abubuwan da yayi mata, idan har zata iya sadaukar da lafiyarta domin ceton shi, meyasa zai ci gaba da tsanarta? Shin mai tayi masa? Meyasa ya kasa fahimtar zuciyarta? Wacce iriyar soyayya take mishi har da zata iya bada ƙodan ta gare shi duk da ƙiyayyar da yake mata? Ya shiga ruɗani da rikicewar zuciya, Zama yayi sai dai ya kasa cin komai a wurin yana jiyo maganganun Momy da take yi wa Maryamun Tana tambayarta jikin nata, a cewar ta, "in har bata ji sauƙi ba zata saka SHAREEF yakai ta asibiti yanzu a duba ta." Amma sai Maryamun tace, "a'a da sauƙi jikinta, maganin yana mata aiki ta soma jin sauƙin kan." Ya kasa cin komai haka ya tashi jiki a sanyaye ya nufo wurin su yana cewa, "Momy zan wuce." "Ok to Allah ya tsare ya bada Sa'a." "Amin Momy na gode." Yayi maganar idanunsa a kan Maryamu da har yanzu ta kasa ɗago kai bare ta kallesa, Har yabar wurin bai samu sun haɗa idanu ba Yana fita sai Maryamu ta kalli Momy tace mata, "tana son koma wa Abuja a yau, ta gaji da zama nan." Da mamaki Momy take kallonta, tace, "kamar ya kin gaji da zama a nan Maryam? Ko wani abun ake miki baza ki zauna ki ƙarisa hutun ki ba?" "A'a Momy Ni dai kawai a mayar dani can, ko kuma in koma Zaria in ƙarisa hutun, ba na son zaman nan." Shiru Momy tayi tana duban ta, domin tabbas ta fahimci akwai tsantsan damuwa a tattare da ita a yanda take maganar dole akwai wani abun a ranta, dalilin da yasa tace, "ko dai SHAREEF yayi miki wani abun ne kike son tayar da hankalin ki Maryam?" Kamar zata yi kuka tace, "a'a Momy..." Sai tayi shiru ta kasa ci gaba da maganar Itama kuma Momy tayi shiru tana ta kallonta, Hakan ne yasa Maryamu ta duƙar da kanta saboda ganin yanda ta ƙura mata idanu, "Shikenan, bari zan sanar da Dadyn ku in ya amince sai driver yakai ki ko zuwa anjima ne, bari Sadiq ya shigo gidan shima ya je wurin Abokansa ne sai ku je ku sake wasu siyayyan ki yi musu tsaraba." Jin haka har zuciyar Maryamu tayi dama-dama ta soma jin sanyi, domin a yanzu ba ta buƙatar ci gaba da zamanta a gidan nan, koda wasa ba ta son sake tozali da fuskar SHAREEF kuma a wannan lokacin, farin cikin ta kawai ta samu tabar gidan nan batare da sun sake haɗuwa ba, domin a yanda take ji komai zai iya faruwa da ita, ranta a ƙuntace take burin ta kawai tabar gidan.*** Ai kuwa zuwa ƙarfe ɗaya Maryamu ta haɗa kan kayanta kaf, tunda Dady ya amince sabida yanda suka ga ta matsa tana son tafiya, shima tunda ya tambaye ta ta nuna tana son tafiyar ne kawai, hakan ne yasa ya yarda, suka fita da Sadiq suka sake yin siyayya sannan suka dawo gida, bayan ta gama haɗa kayan ta tayi sallan azahar sannan suka durfafi hanya da driver, sai Abuja. Koda su Hanif suka dawo sai dai suka ji labarin tafiyar ta a bakin Momy. [17/04, 3:56 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE20* _____Maryamu ta tafi da kwana huɗu; shima Sadiq ya wuce England; tare da Hanif suka tafi, Dayake shi zai je yayi masa wasu abubuwan na harkan karatun, bai dawo ba sai da ya tabbatar da ya kammala masa komai before ya dawo A lokacin Dady yake sanar masa, "ya gama binciken neman auren sa, a koyaushe za a iya tura wa, don haka yanzu babu wata matsala sun gama yarje mishi aurenta." Sosai Hanif yayi farin ciki matuƙa, domin har ga Allah bai da burin da ya wuce yanzu ya samu Amra a cikin gidan sa, soyayyar da yake mata bana wasa bane, bare yanda ya haɗe da tausayi, yana tausaya mata ko don rashin maganar nan nata, don haka a yanzu ya saka a ransa da zaran sun yi aure zai nema mata magani Insha Allahu, ko Allah zai sa a dace, duk da bai taɓa maganar da ita ba bare ya tuntuɓe ta ko an taɓa nema mata magani ne a baya, yabar dai maganar zuwa bayan bikin su Amma sai dai kuma matsalar da suka soma fuskanta, iyayen Amra ƴan uwan Mahaifinta sun ƙi amince wa da auren, musamman da Baba Jafaru ya gane Hanif ne zai aure ta, sam ya ƙi amincewa tunda shine babba a cikin su, shine mabi da Mahaifin su Amra, kuma a yanzu tunda ya yanke hukuncin baza a bada auren ba, sai sauran ƴan uwan suka goya mishi baya, yayi ruwa yayi tsaki yace, "in har ba Jabir zata aura ba, wlh baza su taɓa bada auren ta ba." Abun fa har ya zama fitina, don har maganar takai ga mai anguwan garin su, tunda Dady ya dage baza a tauye wa yarinyar haƙƙinta ba, tunda ya gane halayen Baba Jafaru shiyasa ya dage sai ya amsar musu ƴancin su, musamman da ya zauna da Amra da Mama ya ji ta bakin su, kuma yayi musu alkwarin, "Insha Allahu zai tsaya musu, bazai taɓa bari a cuce su ba." Dalilin da yasa yakai ƙaran su kenan har hukuma suka sake shiga maganar, sanadin da Mai anguwan garin yace, "shi zai zame mata waliyi in an zo auren, kuma da sa hannunsa a tsayar da baikon su." Haka kuwa aka saka ranan auren nan da watanni bakwai masu zuwa, wanda yayi dai-dai da kammala karatun Haseena za a yi bakin tarewan su tare Duk yanda su Baba Jafaru suka so su tayar da ɓalli su nuna su ne dolen su Amra, amma abun ya faskara tunda an shigo da hukuma ciki, amma sun yi rantsuwa, "in har su zasu yi musu aure, to wlh ba da yawun su ba wannan auren, su je suyi duk abun da suke so sun cire hannu a kansu." Dady kuma yace, "ya dauki maraichin su, shi zai zame musu Uba daga nan har Allah ya ɗauki ransa, Insha Allah baza su taɓa maraichi ba, duk abun da suke so shi zai yi musu." Ba ƙaramin farin ciki suka yi ba, domin har gida Mama ta zo ta yi musu godiya har da Momy, tare da su Amran ta zo suka zo suka nuna musu farin cikin su Ita kanta Momy ta yaba da tarbiyyar Yaran, ba ƙaramin dad'i ta ji ba da ta ga yarinyar da Hanif zai aura, kuma ta yaba da kyawun ta, babu wani abun kushe wa a tare da ita in ba an faɗa maka tana da laluran magana ba, don a lokacin ji take yi tamkar su barta a hannunta ta zauna tunda ta shiga ranta, amma dai haka tabar abun a ranta tayi musu sha tara na arziki, yayinda Hanif ya mayar da su gida, Ba abun da su Mama zasu yi wa Ahalin Hanif da shi kansa domin nuna musu godiyar su, domin basu da abun da zasu saka musu, haƙiƙa sun taimake su a lokacin da suke neman taimako, Allah maji roƙon bawan sa ne tunda har ya amsa roƙon su ya turo musu bayin Allan nan suka shiga rayuwar su, addu'ar Mama a kullum Amra ta samu inda zata huta da kuma wanda zai tallafi rayuwarta ya riƙe maraichin ta da laluran ta, sai ga shi Allah ya amshi roƙon su, haƙiƙa suna farin ciki a wannan lokacin tunda basu rasa komai ba albarkacin waɗannan bayin Allan da suka shigo cikin rayuwar su, basu da bakin musu godiya su wadatar da su To tun daga nan haka rayuwa ta ci gaba da tafiya, yayinda a gefe ɗaya Hanif da Amra soyayyar su sai abun da ya ci gaba, suna kaunar junan su sosai, a kullum burinsu su faranta wa junan su rai, duk abun da yasan Amra zata nema a duniya yana iya ƙoƙarinsa na ganin yayi mata shi ko mene ne, koda bata ce ba in har ya ga abun zai dace da ita yana siya ya mallaka mata, kuɗin da yake kashe wa a kan Amra ba ƙaramin girgiza su yake yi ba Ita kanta Amran tana gaya masa, "ya dena mata irin waɗannan ɗawainiyar, ya bari idan ya aure ta ko mene ne sai yayi tunda ta zama nashi, amma abun yayi yawa yanzu." But ba ya sauraron ta, bai fasa alherin da yake musu ba, domin yana ji ko nawa ne zai iya kashe wa a kanta, ita kaɗai ce Macen da yake jin ta shiga ransa fiye da ƴan matan da yayi a baya, yana matuƙar tausaya mata, yana tsananin ƙaunarta sosai, a kullum nuna mata yake yi domin ba kaɗan ba Hanif ya iya soyayya, yana faranta mata matuƙa, Har tana jin cewa babu wata Macen da ta fi ta sa'ar Miji, a yanzu tana jin cewa ita ce ƴar baiwa fiye da kowanne mutum a duniya, haƙiƙa Allah ya ɗaukaka ta babu abun da zata saka mishi dashi sai biyayya gare sa da kuma nuna godiyarta da a kullum cikin ranta ba ta gushe wa da furta alhamdulillah sau babu adadi, Allah shi ne gatanta kuma ga shi ya bata Mijin da tana jin baza ta taɓa samun wani bayan shi ba, ya ɗauki ɗawainiyar ta kuma ya ɗauki na ƴan uwanta, da mai zata saka mishi? Bata da sauran baƙin ciki a yanzu, shiyasa take mugun sonshi, tana mishi soyayyar da bata taɓa tunanin zata yi wa wani ɗan Adam ba, haƙiƙa dukkan su suna cikin farin ciki duk makusantan su sun san da haka Musamman ma Hanif, a yanzu shi ya zame hannunsa gaba ɗaya a kan SHAREEF, ba ya kula sa balle ya damu da sha'anin sa, tunda duk wani shawara da zai ba shi ya rigada ya ba shi but ya ƙi aiki dashi, sai dai ya zura wa sarautar Allah ido, ya ƙyale sa yayi duk abun da zai yi, shi dai a yanzu yana farin ciki kuma ba ya son abun da zai daƙile mishi duk wannan farin cikin nasa Dama ai haka soyayya take, wasu ta sanya su cikin farin ciki da nishaɗi, su ji kamar babu wanda ya fi su dace da Abokin rayuwa na gari, wasu kuma akasin haka ne, yayinda Allah zai jarabbe su ta fannoni kala-kala, Yanzu dai SHAREEF yana cikin wannan jarabawar da bai san ranan fitan sa ba, domin a yanzu bai da wani sauran sukuni, kawai rayuwa yake yi amma babu farin ciki bare nishaɗi a zuciya, sai dai yana iya bakin ƙoƙarin sa wajen ɓoye halin da yake ciki. *** A can kuwa fannin Maryamu tabbas ta share babin SHAREEF na har abada a cikin rayuwarta, ada tana jin baza ta iya rayuwa babu shi ba, amma a yanzu komai ya sauya, kamar yanda ya nuna mata ɗabi'un sa ya muzguna mata bai tausaya mata ba, tabbas tayi imanin baza ta taɓa farin ciki da samun sa ba, a yanzu babu wani ɓurɓushin soyayyarsa, sai ma zallan ƙiyayyarsa da take jin a koyaushe yana mamaye mata ilahirin zuciya, tsab ta kulle shafin sa karatu kawai ta saka a gaba shine burinta a koyaushe Suna cikin tsaka da karatun ne aka aiko Bintu ta haihu ɗa namiji, Sai dai babu damar da Maryamu zata je duk da ta ci burin zuwa duk sanda ta haihu, amma kuma sabida karatunta bazai yiwu ta tafi ba, A lokacin suna tsaka da karatun su ne, babu jima wa suka zana jarabawa suka samu Hutu a time ɗin Sai dai bata samu damar zuwa ba har suka gama hutun suka sake koma wa school, suka ɗaura karatun su, wanda daga wannan hutun ne kuma sun gama da SS 2, in sun dawo zasu shiga ajin ƙarshe, abu kamar wasa, dama komai lokaci ne, duk abun da ake nema wata rana za a cin masa Ga shi yau da gobe itama Haseena har ta kammala karatun ta ta dawo gida, sai dai fa a inda gizon ke saƙan, kuma rigimar take, yadda ta dage tace ma Mahaifinta, "zata koma can ta ɗaura karatun ta na master's, don baza ta iya zama a nan ba, can take son zuwa ta ci gaba da karatu." Kuma a wannan lokacin take bukatar komawa, cus tayi musu ƙaryan, "tana business a can ba ƙaramin kuɗi take samu ba." Su kansu sun san Haseena ta sauya sosai, musamman yanda take jiƙa su da kuɗi tayi ta tura musu kuɗaɗe shiyasa suka amince da cewan sana'a take yi kamar yanda ta ɗaura su a kai, sun hau sun zauna sun amince da ita, Sai dai Ummansu ne ta ƙi amince wa da komawar ta can abroad ta ci gaba da karatu tunda da auren SHAREEF a kanta, gwara kawai ta tare hakan zai fi, inyaso tayi karatun ta a nan, daga nan har ta ga ƙarshen biro wanann ba damuwarsu bane Amma sam Haseena ta nuna ba ta so, ita can take son tafiya ko don business ɗin da take yi yanzu, kuma actually sabida Nana zata koma can da zama a nufin zata je ta ci gaba da karatu, dama ko da yardan iyayenta ko babu yardan su baza ta taɓa yin nisa da Nana ba, a yanzu baɗalar da suke yi abun yayi tsamari babu yanda za a yi suyi nisa da juna har wani lokaci, already rayuwar can ya ruɗe ta don ji take yi baza ta iya zaman Nigeria ba, duk wani wayou dole ta yi wa iyayenta ta tafi, SHAREEF kuwa ba a maganar sa don bata da matsala dashi, ko ya yarda shima ko kar ya yarda zata yi tafiyar ta ne, amma bai isa ya ja da zancen ta ba tunda ta san bazai taɓa dena sonta ba To Abbanta ma ya goya mata baya tunda shi bai damu ba in har zata je karatu ne, dama tun farko ita ta matsa aka yi auren, to yanzu shi da kansa ya yarje mata ta tafi, idan ta gama sai a yi bikin auren su, Da kansa ya kira Abokin Dady; Doctor Umar da kuma babban Yayan su Momy, waɗanda su suka zo suka nema wa SHAREEF auren ta, don haka su ya samu ya faɗa musu halin da ake ciki yanzu, a cewar sa, "idan ta je tayi master's ɗin ta ta dawo sai ta tare, in zai iya jira to ya jira ta, domin shi a wurin sa bai da burin da ya wuce ya so abun da ƴarsa take so." A lokacin da suka je wa Dady da maganar, yayi shiru ya kasa ce musu komai, amma abun ya ɗaure masa kai kuma ya sha mamaki matuƙa, Shi yasa da kansa ya samu SHAREEF ya sanar mishi yanda aka yi, tunda Haseena bata faɗa masa komai ba har ta koma can Australian Hankalin SHAREEF ba ƙaramin tashi yayi ba, ya kasa ma ƙwaƙƙwaran motsi bare ya san mai zai yi a lokacin, zuciyarsa kamar zata faso ƙirjinsa don zafi da tuƙuƙin da take mishi, ga zufa na keto mishi jikinsa sai rawa yake yi ransa yayi matuƙar ɓaci, wai mai Haseena take nufi dashi ne? Mai take so a gare shi wanda bai mata ba ko kuma bazai mata ba har ta sauya mishi haka? Taya ya zai iya jure wa kuma ya sake jiran ta har ta gama wasu shekarun before ta tare? Dady yace mishi, "tun farko abun da muke nuna maka kenan amma ka kasa gane wa, Ni a ganina har da rashin yin mana biyayya shiyasa komai naka ya taɓarɓare haka, ita wacce kake so ga shi ba takai take yi ba, hankalin ta yana can wani wurin, to Ni bazan zura maka idanu kayi abun da kake so ba, ko ka nemo wata matar a ɗaura auren tare dana ɗan uwanka, ko kuma ka amshi zaɓin mu, shawara ya rage naka, ka je kayi tunani, amma ba yanda za a yi mu zuba maka idanu ka ci gaba da zama babu aure alhalin kullum cikin ciwo kake, daga ƙarshe in ka kamu da wani mummunar ciwon dole mu zamu yi jinyar ka, SHAREEF a yanzu umarni nake baka wlh idan har baka yi ɗaya daga cikin abun da nace maka ba, ranka zai yi mummunar ɓaci, zan nuna maka wane ne Ni a wannan lokacin, kallona kawai kake yi baka sanni ba tunda baka san abun da yakamata da kai ba, ita kuma yarinyar tunda baza ta zauna da kai ba, ka sake ta don ban ga amfanin ci gaba da zama da auren ta ba. Ka tashi ka ɓace min a nan." Ya daka masa tsawa ransa a mugun ɓace Da sauri SHAREEF ya tashi ya wuce dakinsu, sabida tashin hankali ma ba ya iya ganin gabansa tafiyar kawai yake yi tamkar zai kifa don sauri, ikon Allah ne kawai ya kaisa cikin dakin su.*** Dayake babu Momy a wurin ta shiga ɗaki ta dawo, koda ta dawo Dady ya zayyane mata abun da ke faruwa na zuwan su Doctor Umar da abun da suka faɗa mishi, da kuma hukuncin da ya yanke a kan SHAREEF Ita kanta bata ji daɗin abun ba domin ranta ya ɓaci matuƙa, amma sai tace, "wlh koda SHAREEF ya amince da Maryam baza ta taɓa tarewa ba, tunda tun farko mun nuna mishi abun da ya dace ya ƙi bin umarnin mu, don haka a yanzu ba yanda za a yi mu tauye mata haƙƙinta, yanda take karatun ta cikin kwanciyar hankali haka zata ƙare shi ya je can da tsiyan sa, ita yarinyar da ya zaɓa ya je can ya ci gaba da jiran ta. Ato Ni dai baza a tauye wa Maryam haƙƙinta ba, karatu kuma baza ta bar shi don yanzu ya rasa wacce yake so ba." "To yanzu mai kike so a yi ne Deeja? Idan ya nuna da ita zai zauna ya haƙura sai kuma mu hana sa Matarsa? To mene ne amfanin zaman da take yi da auren sa wai?" Shiru tayi tana tsuke fuska, sai tace, "Ni a ganina SHAREEF bazai amince da ita ba har wannan lokacin, abun nufin kawai a raba auren tunda babu lallai babu tilas sai sun zauna tare." Da mamaki Dady yake kallonta, "haba Khadijah ya za a yi ki ce a raba auren? Taya ya na ɗauko yarinya daga gaban iyayenta sun amince da Ni har suka ba ɗana auren ta, duk tsawon wannan lokacin basu san mai ke faruwa ba, sannan kuma a yanzu in je musu da batun ya sake ta, da wanne idon kike so in kalle su? Ai bazai ma yiwu bane, domin a auren nan babu saki an yi shi kenan, SHAREEF bai isa ya watsa min ƙasa a ido ba, abun da yasa tun farko ban matsa mishi dole sai ya zauna da ita ba, don kawai na ga ita yarinya ce bari nake yi tayi karatun ta ko secondary ne ta gama, ba wai na ƙyale sa haka kawai bane, don haka ki dena tunanin ma auren nan za a raba shi, tunda aka yi shi Insha Allahu sai SHAREEF ya zauna da ita ko ba ya so wlh."*** Kuka SHAREEF ya fashe da shi a time ɗin da ya shiga cikin ɗakin su ya zube a Falon, yayinda ya haɗa kai da gwiwa cikin tsananin ɓacin rai da baƙin ciki ya kasa jure abun da yake ji, hakan ne yasa kukan ya kufce mishi ya kasa dakatar da kansa daga raɗaɗin da yake fama dashi Hanif na bedroom yana barci, kukan SHAREEF ya farkar dashi, daga inda yake yana jin shashsheƙan kukan sa, wanda hakan ne ya ba shi mamaki da sauri ya sauko ya nufo Falon don ya ga wane ne ke kuka? For surprise SHAREEF ya gani zaune a ƙasa ya haɗa kai da gwiwa yana gunjin kukan, abun ya mugun ɗaure masa kai, kuma hankalin sa yayi tsananin tashi, da gudun sa ya isa inda yake yana zube wa a gabansa, hannunsa na rawa wajen ɗago kansa da faɗin, "Bro, mene ne hakan? Me ya faru ne? Don Allah ka sanar min ko wani abun ya samu su Momy ne? Why are you craying?" Ɗakyar SHAREEF ya ɗago kansa yana duban Hanif, idanunsa sun yi wani irin girma ga hawaye yanda suke shatata sun kasa tsaya wa, haka shi kansa ya kasa yin magana sabida yanda jikinsa ke rawa haka laɓɓansa, wani abu ya tokare mishi maƙogwaro ya kasa buɗe baki bare ya yi wa Hanif bayanin da yake son yin masa Wanda shi kuma hankalin sa ƙara tashi yake yi duk ya bi ya dame sa da tambayoyi, gaba ɗaya ya ruɗe domin tunda yake bai taɓa ganin SHAREEF yana kuka wi-wi haka ba, gabansa buga wa yake yi don babu abun da bai bijiro masa a cikin zuciya ba, so yake yi ya tashi ya je ya duba su Momy ko wani abun ne ya same su, amma kuma ya kasa sai tambayar SHAREEF yake yi hankalin sa a matukar tashe "Hanif ban san yanda zan yi ba, Haseena ta cuce Ni ta gama dani." Sai yayi shiru ya kasa ci gaba da maganar illa rufe idanuwansa da yayi har yanzu suna tsiyayar da ruwa Da mamaki Hanif kuma yake kallonsa, sai yace, "i don't understand you Bro, mai Haseenan tayi kuma?" Ɗakyar ya buɗe bakinsa da suka yi masa nauyi laɓɓansa suna kerma; har ya iya koro masa labarin komai Yayinda tausayin sa ya cika zuciyar Hanif, amma sai ya maze yace, "to mene ne abun damuwa Bro? Wai sabida hakan ne ka zo kana wannan kukan; haba Brother da girman ka? Ina ga ai kamar yau ne zata ƙare karatun ta kuma dawowa gare ka. Sai ka jira ta kawai." Wani kallo SHAREEF ya watsa mishi wanda yasa dole yayi shiru yana murmushin gefen baki, Sai kuma ya taɓe baki yace, "ai gaskiya na faɗa maka." Jiki a sanyaye SHAREEF yace, "I know gaskiyar su Momy ne, abubuwan da suke faɗa min, a yanzu dai na san cewa Haseena ta dena so na, ba na gabanta." Sai ya ɗago jajayen idanunsa ya zuba wa Hanif da shima ya ƙure sa da kallo, cikin takaici da ɗacin zuciya yace, "but har yanzu ina jin ta a raina, soyayyarta a kullum ƙaruwa yake yi na kasa haƙura da ita, please help me bro I don't know how to remove her from my heart, I want to forget her forever, please help me." Yanda ya ga yana tsiyayar da hawaye ba ƙaramin tausayin sa yake ji ba, da sauri ya kama hannayensa biyu ya haɗa da nasa ya dunƙule su, yayinda suke kallon idanun juna, murya a sanyaye Hanif yace, "addu'a kawai zaka riƙa yi har Allah ya yaye maka soyayyarta, a yanzu dai babu amfanin ci gaba da sonta, wurin Allah zaka nemi taimako Bro tun kafin lokaci ya ƙure maka, ka sani cewa idan ka ci gaba da zama a haka kana ɓata wa Iyayenmu baza ka taɓa ganin dai-dai ba, You know a koyaushe ina faɗa maka har alhakin Maryam zai iya bibiyan ka muddin baka gyara tsakanin ku ba, ita ce wacce ta dace da kai, da ita yakamata ka zauna don ita ce masoyiyarka na haƙiƙa, soyayyar da take maka har ta iya sadaukar da wani abu mai muhimmanci a gare ka, amma ka kasa fahimtar zuciyarta, kayi tunanin yanda kake jin ƙuncin nan; haka itama take fama dashi, kai namiji kenan a yau ga shi kana kuka a kan wata, to bare Ita Mace mai rauni, Bro koda baza ka so ta ba don Allah ka cire ƙiyayyarta a zuciyarka, mai ta taɓa maka da zafi da har kake jin zaka muzguna mata don kawai ta nuna maka ƙauna?" Sai yayi shiru yayinda idanuwansa suke ci gaba da yawo a cikin na SHAREEF Shi kuma jikinsa yayi sanyi idanunsa sun sake kaɗa wa domin har lokacin hawayen ciki basu dena zuba ba, tabbas a yanzu babu wannan tsana da jin haushin da yake mata, tun lokacin da Hanif ya faɗa mishi cewan ita ta sadaukar da ƙodan ta har aka sanya mishi; daga lokacin ya dena jin tsanarta a ranshi, haƙiƙa a wannan lokacin yana tsananin nadamar abubuwan da ya aikata mata, amma bai san ta yanda zai yi ya gyara ba, shiyasa ya binne abun a ransa har zuwa wannan lokacin abun na cin sa a rai, Shiru yayi yana jin zuciyarsa tana kai kawo tare da bugawa da ƙarfi, yana sauraron zantukan Hanif da ke ta ba shi shawarwari na tsawon lokaci ya gaza yin shiru, Bai da kuma wani buri a yanzu da ya wuce ya rabu da soyayyar Haseena ko zai samu salama a ransa, Yana son ko ya ya ne ya saka soyayyar Maryamu a cikin ransa, duk da a yanzu babu sonta amma babu ƙiyayyarta, tabbas ta cancanci ya so ta ya ajiye komai a gefe To daga wannan ranan sai SHAREEF ya soma fafutuka domin ya ga ya rabu da Haseena, sabida a yanda yake jin soyayyarta ba ya jin zai iya son wata Mace har ya haɗa su wuri ɗaya a cikin zuciyarsa, wannan dalilin ne yasa da kansa ya yi wa kansa faɗa wurin gyara ibadarsa da Allah, Ada ba ya zama yayi wata doguwar addu'a don yayi sallah, sallan ma ba ya yin ta a kan lokaci sai idan ya ga dama, amma a kwanakin nan sai ga SHAREEF ya sauya sosai, don shi kansa yana jin baƙin cikin yanda ya kasa manta wa da Haseena, koyaushe soyayyarta ƙaruwa take yi, kamar yanda Hanif ya ba shi shawara ne, idan ya tashi tsaye wurin roƙon Allah Allah zai yaye mishi damuwarsa, To SHAREEF dai ya soma hankali, har idan yayi Sallah zaka ga ya zauna yana kai kukansa wurin Allah subhanahu wata'ala domin ya yaye masa abun da ke damun sa, Duk da babu wani canji amma ya soma samun natsuwa ba kamar baya ba da kullum bai da sukuni zuciyarsa tana mishi zafi da ƙunci, amma yanzu yana iya jure komai yana samun sauƙi a zuciya, Kuma a yanzu ya gama yanke hukuncin amsar zaɓin iyayensa hannu bibbiyu, don yana ji a ransa Maryamu kaɗai ta dace ya zauna da ita ko domin yin ma iyayensa biyayya, Duk da yanzu Dady bai sake mishi magana ba, amma ya yanke shawarar idan ya neme shi zai sanar musu ya amince da zaɓin su Lokacin da ya sanar da Hanif ba ƙaramin dad'i ya ji ba, har rungume sa yayi ya taya sa murna yana ta jin dad'i, don bai da buri sama da ya ga SHAREEF ya so Maryamu, to a yanzu ga shi komai yayi sauƙi tunda har da bakin sa ya faɗa masa zai zauna da Maryamu zai bi zaɓin iyayensu.*** Yanzu haka saura sati biyu bikin Hanif ɗin, Kuma lokacin yayi dai-dai da samun hutun su Maryamu, Don haka koda suka samu Hutu gaba ɗaya suka taho Kano biki. [19/04, 7:18 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE21* _____SHAREEF sai a wurin Hanif ya ji labarin zuwan su Maryamu, lokacin sun taso daga wurin aiki yake faɗa masa isowar su, da nufin ya ji ta bakin sa Amma SHAREEF bai ce komai ba har suka dawo gida, to bai san mai zai ce ba, amma har zuciyarsa yana jin farin ciki da jin labarin, kawai ya maze ne ya nuna kamar maganar bai dame shi ba, nan kuwa cike yake da son ganin Maryamu wacce yake mamakin taimakon da tayi masa duk da irin tsanar da yake nuna mata Dukkansu suna zaune a falo ban da Dady da shi ba ya gidan a lokacin, A tare suka shigo Falon dashi da Hanif da sallama a bakin su Da gudu Na'ilah ta nufo wurin su tana musu oyoyo, amma lokacin da ta iso wurin su sai ta tsaya kuma tana kallon su ta rasa wurin wanda zata je Hanif ɗaukar ta yayi yana shilla ta sama; cikin farin ciki yake cewa, "Oyoyo My Na'ilah, yau ga Na'ilah a gidan mu." Sai dariya take yi tana washe baki cikin tsantsan farin cikin ɗaukar ta da aka yi, dama abun da take so kenan While SHAREEF kuma ciki ya nufa idanunsa tuni sun sauka a kan Maryamu Wacce suke zaune su uku a saman three sitter, Aakifah na tsakiya, ita da Yusaira suna gefe suna taɗin su cike da nishaɗi, But ita tunda ta ga shigowar su sai ta kawar da kanta a wurin su bata sake kallon inda suke ba Aakifah tare da Yusaira suka yi wa SHAREEF sannu da zuwa tare da gaishe shi dukkansu fuska a washe Ya amsa su shima face ɗin sa a sake, before ya nemi wuri ya zauna yana gaishe da Ammee Ta amsa itama da fara'a tana cewa, "kun ga baƙin bazata, kuna wurin aiki ko huta wa ba kwa yi, har da kai Ango? Maimakon mu tarar da kai a gida wato?" Ta ƙare maganar tana kallon Hanif da ya iso wurin su ya sauke Na'ilah, Sai ta nufi wurin SHAREEF ta ƙanƙame shi tana dariya, "Ammee ina wuni kun zo lafiya?" "Alhamdulillah Hanif, ya shirye-shirye ya kuma aikin?" Yana shafa kansa cike da kunya yace, "Alhamdulillah Ammee, ina Abee bai zo ba?" "Abee ai ba yau ba, sai ranan biki zaka ganshi Insha Allahu don yana gari." Gaishe shi su Aakifah suka yi Idanunsa ya mayar kansu, sai kuma ya miƙa musu hannu dukka suka tafa har Maryamu Tana dariya tace, "kai Yaya wlh har ƙyallin angwanci ka fara. Askin nan ba ƙaramin kyau yayi maka ba. So good my lovely Bro." Dukka dariya ta basu sabida tayi maganar har tana huro mishi kiss Shi kansa SHAREEF abun ya burge shi, sai dai ko kaɗan bai nuna a kan fuskarsa ba, amma idanunsa yana a kanta yana ɗan satan kallonta, sosai yake mamakin yanda ta ƙara sauya wa fiye da wancan zuwan da tayi, a sace yake kallonta don kar su Momy su gane, kuma ya kasa tashi ya wuce ɗakin su haka nan ya zauna a wurin yana sauraron hiran nasu da ya kasa saka baki a ciki, abun mamakin yanda ya ji Maryamu take ta zuba ta fi kowa surutu a cikin su, shi dai tunda ya santa bai taɓa ganin tana magana sosai ba, zai iya cewa bai gama sanin muryanta ba ma, bai san cewa tana da surutu har haka ba sai yau da dalili yasa shi zama yana sauraron ta, dalili kuwa na rashin jin tsanar ta da yake yi a yanzu wanda yasa har burge sa ta fara yi, ya santa da shegen kallo kamar zata cinye Mutum, amma abun mamakin yau yana son su haɗa ido but ko kallon inda yake bata yi ba, in fact ma ko gaishe shi bata yi ba, hakan ba ƙamarin tsaya mishi a rai yayi ba, Ya kasa tashi bare yabar wurin, yana zaune yana sauraron su, Na'ilah na jikinsa yana mata wasa ya miƙa mata wayansa suna danna wa a tare, babu wanda zai yi tunanin hankalin sa yana a wurin ma Har aka kira sallan Magriba suna a wurin suna ta hira, sannan suka tashi sabida yin Sallah Sai a lokacin SHAREEF ya samu ya wuce ɗakinsu ya bi bayan Hanif da shima tuni ya shige, Bayan sun yi alwala suka fita sallah, Lokacin Dady shima ya dawo shima tare da shi suka tafi masallacin After sun dawo suka zauna a falo gaba ɗayansu har su Ammee da suka fito sun idar da nasu sallan Momy kuma ta shiga kichen ita da Maryamu da ta bi bayan ta; don ta taya ta ƙarisa haɗa abincin da suka gama, ba don komai ba don kar ta zauna wurin da SHAREEF yake shiyasa ta nufi wurin Momy tana taya ta kwashe abincin, Bayan ta zuba a coolers sai ta kwaso takai saman dining, Momy tabar mata sauran aikin ta ƙarisa sannan ta zo ta zauna cikin su Dady yace, "My daughter taho nan kusa dani ki zauna, nayi kewar ki sosai fa, mun yi magana da su Innan ki ma, suna kan hanya zasu zo bikin suma." "Don Allah Dady da gaske?" Tafaɗa cikin farin ciki tana nufan sa Dariya suka yi, Dady shi kuma yana ƙara bata tabbacin hakan, "suna kan hanya Insha Allahu haka Babanku yace min, dukkan su zasu zo." Sosai Maryamu tayi farin ciki, don ta kasa ɓoye hakan a kan fuskarta, Sai kuma tace, "Dady amma in sun zo zan bi su kawai mu tafi tare, sai in yi hutuna a can." "Duk yadda kike so my daughter bazan hana ki ba. Deeja, a kawo mana abincin mu nan mu ci ko, don zai fi dad'i a nan ɗin babu takura." "To." Momy ta amsa mishi tana shirin tashi Sai Ammee tace mata, "ta zauna, su bari su kwaso." Kallon su Aakifah tayi tace, "ku tashi ku je ku kwaso abincin ku kawo nan." Umarnin ta suka bi zuwa wurin dining ɗin, suka kwaso abincin, ita kuma Maryamu ta ɗauko abun shimfida wa; aka shimfiɗa a wurin, Ammee da Momy suka yi save din su While SHAREEF ne kaɗai ya nuna bazai ci ba, ya fi son tea Ammee ta dubi Maryamu tace, "Maryam, haɗa masa tea mana, sai ki kawo masa." Sai lokacin Maryamu ta kalli inda yake, a karon farko suka haɗa ido dashi, ganin yanda idanuwanta suka shige cikin nasa shiyasa ta haɗe fuska tana miƙe wa ta wuce zuwa kichen, a ranta tana jin haushin saka ta aikin da aka yi Shi kuma ganin haka sai ya mike da wayansa a hannu kamar yana waya ya wuce zuwa ɗakin sa Koda ta kawo tea ɗin babu shi, baƙin cikin yanda Ammee tace mata, "takai mishi yana ɗaki." Kamar ta kurma ihu, amma sai ta juya ta wuce saman zuwa dakin nasu, ko sallama bata yi ba ta zura kanta ciki fuskarta a haɗe babu fara'a, Ganin sa tayi zaune a kan sofa yana faman latsa wayansa, Wurin sa ta nufa ta ajiye mishi a saman Centre table tana ƙoƙarin juya wa, Sai jin murynsa tayi ya tsayar da ita, kamar kar ta tsaya, sai kuma ta ja ta tsaya tana juya wa da duban sa, ido cikin ido suke kallon juna babu tsoro ko shakkar sa a tare da ita, don a yanzu yadda take jin muguwar tsanar sa komai zata iya faɗa mishi babu kunya bare tsoro, har da wani kama ƙugu tana karkaɗa jiki da jiran abun da zai faɗa mata Shi kuma dayake bai da bakin magana, bai ma san mai zai ce mata ba, kawai dai ya dakatar da ita ne don ya ci gaba da kallonta yana ƙare wa halittar jikinta kallo, wanda ba ƙaramin tafiya dashi tayi ba da shigan da tayi, Atamfar da ta sanya yayi mata kyau ainun, riga da skirt ɗinkin wanda yayi mata cif kamar an zana a jikinta, dayake farar atamfa ce da ratsin orange colour kuma ɗinkin zamani, sannan tayi ɗaurin ture kaga tsiya, skirt din ya fitar mata da shape ɗin ta hips ɗin ta ya bayyana gunun ban sha'awa, face ɗinta tayi fresh sosai babu ko ɗigon tabo a kan fuskarta, sai idan tayi magana dimples ɗin ta su ƙara bayyana tsantsan kyawun ta, a wannan karon shi dai gani yake yi bai taɓa ganin bak'ar fatan da tayi wa wata Mace kyau irin Maryamu ba, very smooth and fresh haka skin ɗin ta yake glow da ɗaukar ido sabida sauyin yanayi da hutun da ta samu, ga manyan idanuwanta gulu-gulu da suka ƙara mata sihirtaccen kyau, sai yanzu yake ganin ainihin kyawun ta da ya kasa fahimta; sai yanzu da babu tsanar ta a zuciyarsa, tabbas ya yarda da maganar Hanif da yace, "there are different between Haseena and her." Ita kuma ganin ya zuba mata idanu yana ƙare mata kallo babu kunya babu tsoron Allah, hakan ne ya bata haushi ta watsa mishi kallo tare da juya wa ta fice a ɗakin bata sake waige ba While SHAREEF kamar ta tafi da farin cikin sa, jiki a sanyaye ya ɗauki cup ɗin ya soma shan tea yana faman tunano ta a zuciya, musamman surar jikinta da ya fi tsaya mishi a rai, Allah ya bata ƙira mai kyau, a fuskar duk wanda ya ganta, sam babu ƙiyayyarta a ransa yanzu, sannan kuma babu soyayyarta sabida har yanzu yana jin kamar Haseena kaɗai zai so a duniya, duk da a yanzu soyayyar da yake mata ba kamar da ba, haƙiƙa ya ga sauyi sosai da yake dagewa wajen addu'a, yana roƙon Allah ya rage masa soyayyarta, ga shi yanzu kusan sati biyu kenan rabon su da waya, kuma bai damu kamar baya ba, kamar yanda ta share shi shima yana ƙoƙarin share ta, idan da hali bai ƙi Allah ya musanya mishi da soyayyar Maryamu a cikin zuciyarsa ba, domin a yanzu bai da masoyiya mai ƙaunarsa kamar ta, tayi abun da ba kowa zai yi masa ba, a kullum yana dana-sanin abubuwan da yayi mata, har yana jin zai iya faɗuwa a gabanta domin neman yafiyar ta, tabbas ya yarda ya amshi failed in dai a kanta ne, duk wani cika baki a baya da yayi a yanzu yana dana-sani, musamman yanzu da yake ganin kamar babu shi a gabanta, amma yana ji a ransa har yanzu tana sonshi, kawai ta ɓoye hakan ne domin ta ƙuntata mishi, sai yayi murmushi a fili ya furta, "bakin da ya furta so, har abada bazai taɓa furta ƙiyayya ba, a yanzu na shirya tsab domin kasancewa da ke, kuma dole zan sanar da Dady haka, babu amfanin ci gaba da wannan damuwar, bayan ga ki ina kallo a cikin idanuwana kin haɗa komai inda zan samu biyan buƙata." Sai ya rufe idanuwansa yana jan numfashi mai ƙarfi, "ina matuƙar sha'awarki Maryam, kin soma burge Ni a halin yanzu." Yana nan zaune yana sambatun sa da tunanin banza da hofi, Hanif ya zo ya kira sa a kan Dady na kiran sa, Tare suka koma suka sami Dadyn zaune a falo shi kaɗai, Dayake dare ya ɗan ja kowa ya tafi ya kwanta Shima Dady don yayi magana da su ne shiyasa ya zauna, a kan maganar auren SHAREEF ɗin, yace masa, "wanne hukunci ya yanke? Ya samo wacce zai aura ne ko zai zauna da Maryam ɗin?" Babu musu SHAREEF ya nuna amincewar sa a kan zama da Maryamun Shi kansa Dady yayi mamakin jin furucin sa, sai da ya ƙara maimata masa yace, "ka ce zaka zauna da ita? Ka amince a baka Matarka?" SHAREEF ya sake amsa mishi tare da neman afuwan sa a kan rashin musu biyayya da bai yi ba tun farko, yace, "Dady don Allah kayi hakuri, amma a yanzu a shirye nake da in muku biyayya na amshi zaɓin ku, kawai a haɗa auren mu tare da Hanif itama ta tare, ina buƙatar Matana." Ba ƙaramin dad'i ne ya cika Dady ba, lallai ya yarda SHAREEF ya soma hankali, domin wannan maganar ya faranta masa rai matuƙa, yace, "shikenan Insha Allahu babu damuwa za a haɗa bikin kamar yanda ka buƙata, zuwa ranan asabar ɗin za a haɗa bikinku gaba ɗaya, ka ga yanzu sai ka zaɓi gidan da zaku zauna tunda shi Hanif ɗan uwanka ya zaɓa nasa, inyaso gobe a je a fara gyara a duba duk abun da babu, Allah ya yi muku albarka gaba ɗaya, ku je zan yi magana da Momyn naku, abun da muka yanke gobe zan sake tuntuɓan ku." Daga nan ya sallame su suka tafi, Bayan sun tafi shi kuma ya saka waya ya kira Momy yace, "ta zo tare da Surayya akwai maganar da zasu yi." After sun zo ya zayyane musu komai abun da SHAREEF ya faɗa Dukkansu sun yi farin ciki kuma sun yi mamakin lokaci guda da ya nuna zai zauna da Maryamu, abun da suke fata kenan amma ga shi lokaci ɗaya Allah ya amshi roƙon su Sai dai Momy ta ƙi goyon bayan tariyan Maryamun, tunda a cewar ta, "gaskiya bai kamata a daƙile mata karatun ta ba bayan ta kusa kammala wa, kawai yayi hakuri ta ƙarisa." Dady yace, "a'a, ai kuma bazai yiwu ba, kin san dai yanda muka yi fama da Yaron nan tun a baya bai amince ba sai a yanzu, tunda yana son Matarsa ai kuwa bazai yiwu mu hana sa ba, bare kin san halin da yake ciki ba tun yau ba, da irin ciwukan da yake fama da shi duk dalilin rashin Mata, yanzu kuma ya gane Annabi ya faku ya yi wa kansa faɗa kuma mu ce zamu hana sa? a'a, Insha Allahu Matarsa zata tare a wannan lokacin babu ja da baya, karatunta kuma tunda SS 3 zasu shiga ba sai ta koma ba; idan an zo zana jarabawar fita zata iya zana wa ko a nan ne, shikenan hakan ya fi." Ammee tace, "gaskiya ne Yaya, nima na goyi bayan ka, kawai ta zana jarabawar fita ba sai ta koma makarantar ba, ai abun farin ciki ne wannan." "To shiyasa na kira ku muyi shawara gaba ɗaya, don haka zan sanar da Iyayenta don su san da maganar tariyan ƴarsu, inyaso gaba ɗaya ƴan uwanta sai su taho a yi bikin da su Ni zan ɗauki nauyin zuwan nasu da komawar nasu, itama Maryam Ni zan faɗa mata zan zaunar da ita in fahimtar da ita." Duk sun yi na'am da maganar Dadyn, don haka babu wanda ya ja zancen, bayan sun gama tattauanawa suka wuce suka kwanta. A kwana biyu kuma gidan ya kuma cika ƴan uwan Momy duk sun cika gidan tsaki da ƙwarƙwatan su, dama ba baya ba wurin yawa Ahalin su, bare gidan maiƙo ne babu wanda ya haƙura sai ana gobe biki ko ranan biki, haka suka zo suka cika gidan tun a ranan aka fara hidima da su, komai na biki da ciman da za a ci an fara tanadar wa ana ta aiki a kai The following day kuma sai ga ƴan uwan Dady suma sun zo tsaki da kwarkwatan su, su Aunty Ummita, su Bashir, Matan su Yaya Faisal gaba ɗaya sun tarkato har Yaransu, tunda a kyauta aka taho da su, har can Dady ya aika da Mota yace, "duk wanda zai zo ya zo bai ɗauke wa kowa ba." Tunda ma ya faɗa musu har da tariyan Maryamu, shiyasa suka taho dukkansu, har da Bintu da su Umma Jummai, Innan su Maryamu ma ta biyo su duk da a baya ta nuna baza ta je ba; dalilin sanar musu da aka yi da tarewan Maryamu, amma Dady yace, "ta zo don Allah." Iya Samira ce kaɗai bata zo ba sabida ciwon ƙafa da ya matsa mata, sakamakon hawan jinin ta da ya ɗan tashi a kwanakin, amma zata biyo su Baba in zasu zo a ranan bikin; su da su Yaya Ashiru, su a ranan bikin zasu zo Zuwa sakaliyar la'asar sai ga su sun fantsamo gidan, gida fa ya ƙara cika maƙil A lokacin babu su Aunty Fatima suna can sun je zaɓo wa Maryamu kayan daki, tunda abun ya zo a ƙurarren lokaci, Na Amra kaɗai aka yi tunda Dady ne yayi mata komai, an shirya mata gidan ta tamkar na ƴar gata, Yau kuma aka tafi siyo na Maryamu wacce har wannan lokacin bata san da labarin da ita za a tare ba, za a miƙa ta gidan SHAREEF masoyinta, buri ya cika, sai kwanya ta faɗa. 😳😂💃💃💃 [20/04, 7:17 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE22* _____Maryamu ta ji daɗin zuwan danginta, musamman da ta ga har da Innarsu, shiyasa ta maƙale musu suna tare, Dayake daƙunan ƙasa aka basu a nan suka yaɗa zango, Ire-iren ƴan mata sa'annin Maryamu da su Aakifah, suna ɗakin Maryamun ne su a nan suka kwana ƴan uwan su Momy, har Bintu itama tana cikin su tunda ta ga akwai Maryamu, ga ɗanta da yayi wayon gunun ban sha'awa, sauran cousin ɗin sai mamakin ta suke yi ganin ta ƙarama har da aurenta da Yaron ta, duk da itama auren yasa tayi girma yanzu ta zama Uwa, har ta fi Maryamu tsawon gaɓɓai a yanzu Maryamu a wurin Bintun ma ta soma jin maganar tarewan ta, lokacin suna zaune a ɗakinta suna hira, sauran ƴan Matan suna yi da Bintun har suna cewa, "ai ta huta tayi auren ta yanzu ta huta abun ta." Ana dai ta magana ana raha, Sai Bintun ta raɗa wa Maryamun a kunne tana faɗa mata, "saura ita, nan da gobe zasu kaita ɗakin ta." Kasancewar Maryamu bata da labarin maganar shiyasa bata ɗauki maganar nata da serious ba, sai ma hararanta da tayi tana cewa, "kar ta kawo mata maganar banza, ita da ta zauna a ɗakin Miji sai ta haɗa degree ɗin ta na farko." Su Aakifah suka kwashe da dariya kasancewar sun san halin ta a gida, domin ta sha haɗuwa da Samari idan sun yi mata zancen soyayya ta balbale su da masifa tana gaggaya musu maganganu, A nan fa zancen su Yusaira ya koma kan maganar nata suna bama Bintu labari Bintu tace, "ashe har yanzu halin ta yana nan? Wlh haka take yi lokacin tana ƙauyenmu, ai Samarin garin mu sun sha wulaƙanci, sai ga shi Allah ya cika mata burinta rabon Yaya SHAREEF ne." "Wai wanne Yaya SHAREEF ɗin?" A cewar Yusaira tana gyara zama saboda su har yanzu basu san da auren SHAREEF a kanta ba Dalilin da yasa sauran ƴan matan da suke nasu hiran daban, hankulan su ya soma dawowa wurin su kenan Ita kuma Bintu kamar an buɗe bakin ta tace, "au.. baku da labarin Maryamu tana da aure? Cab ɗijam, to wlh ta riga Ni aure, tun lokacin da aka kawo ta nan da auren ta a kanta, sai da Kawu ya haɗa su aure da Yaya SHAREEF sannan aka taho da ita." Ai nan ta ci gaba da zayyane musu labarin komai tun daga Farko har ƙarshe Mamaki da farin ciki ne ya cika su Aakifah; bakin su har ya ƙi rufuwa, While sauran ƴan matan suma mamakin ne a kan fuskokinsu wannan ya kalli wannan; wancan ta kalli wannan Mubeena wacce take ɗaya daga cikin masu ƙaunar SHAREEF ɗin, sam maganar bai mata dad'i ba, don haka ta riga kowa yin magana tana cewa, "dalla ja can, wacce maganar banza da hofi kike faɗa mana a nan? bayan mun san cewa Yaya SHAREEF yana da Matarsa wacce take zaune a can ƙasar waje; shine za ki haɗa shi da wannan? Kin zauna kina mana tatsuniyar ƙarya mai zai yi da rainon ƙauye." Ta nuna Maryamu sama da ƙasa ranta a ɓace, har da ƙara wa da faɗin, "ko Mata sun ƙare ai Yaya SHAREEF bazai kalle ta ba balle ma ya ɗauke ta a matsayin Mace." Shewa suka saka sauran waɗanda suke baƙin ciki da jin zancen, har suna ƙara wa da faɗin, "faɗa musu dai Mubee, su je wata ƙaryan ba wannan ba, don ta zo tana cin arziki a inuwar su ba hakan yake nufin zata haɗa kanta da su ba, ai na gaba yayi gaba wlh." Ran Maryamu yayi mugun ɓaci musamman maganganun Mubeenan, har ta buɗe baki da ninyar yin magana; sai Yusaira ta riga ta yin maganar "Ai baku sani ba, abun ba daga nan take ba, kun san koda goma ta lallace ta fi biyar albarka, ku dubi Maryam sama da ƙasa takai Macen da Yaya SHAREEF zai iya kalla har ya ƙyasa wlh, ai bai fi ƙarfin yace yana sonta ba shima." Miƙe wa Maryamu tayi a saman kan gadon, tana kallonsu rai a ɓace tace, "bari ku ji da kyau, shi wanda kuke ganin sa wani abu har kuke taƙamar ya fi karfin irina; a wurin ku shine Sarki, amma a wurina ko Bawa bai kai ba bare har ya samu muhimmancin da Maryamu zata zauna tana ɓata lokaci a kansa, ajina da sauran Mata ya sha bamban bare local irin ku masu tunanin shi wani ne a wurin ku, kuma duk ƴar iskan da tace zata gaya min magana a nan wurin; wlh summa tallahi bazan ɗauka ba, tsab zan ci wa kowacce shegiya Uwa a nan, ba a yi dani kuma baku isa ku zauna a gabana kuna maganata ba." Yanda take maganar cikin isa da gadara a kuma fusace, tana girgiza jiki idanu a ware kamar zata cinye su, Sai duk suka shiga taitayin su don har ga Allah ta ɗan basu tsoro Bare ita Bintu ta san halin Maryamu wurin faɗa, yanzu sai ta nemi a ba wa hammata iska don tsab zata iya cewa zata yi faɗa dasu, bata san cewa halin ta yana nan har yanzu ba, shiyasa da sauri ta miƙe tana janyo hannun Maryamun tana bata haƙuri ita da su Aakifah Amma sam Maryamu ta ƙi zama sai girgiza take yi tana ƙara furta, "ku bar Ni don Allah, ai na ga rashin mutuncin nasu a kaina zai ƙare, wani tsiya ne a wurin SHAREEF ɗin da kuke tunanin kowa ma irin ku ne? To ke Bintu ki ƙara maimaita musu da kyau su san cewa akwai auren shi a kaina inga uban da ya isa yace ban kai ba, kuma zan juya shi yadda raina ke so, ko kuma in kun isa ku zo ku kwance auren Ni ce matar SHAREEF, akwai auren sa a kaina ko akwai abun yi?" Itama Mubeenan tuni ta hayayyaƙo mata, musamman yadda Maryamun take mayar musu da martani tana zagin su, tace, "ki tsaya dai a Matsayin ki amma Yaya SHAREEF ya fi ƙarfin ki, a cikin mu babu mai tsoron ki balle ki tsaya kina zagin mu muyi shiru, ko mu da muke rayuwar Hutu da jin dadi; manyan Mata kuma ƴan uwansa na jini, mun fi ki aji da wayewa, kuɗi, nasaba, bai kalle mu ba bare ke wacce a ƙauye ta taso rayuwar ƴan wahala kuma kucakar yarinya." Dirowa Maryamu tayi a kan gadon, tayi kukan Kura sai ga ta a gaban Mubeena, hannu tasa ta shaƙo mata wuya cikin bala'i da masifa; ranta a matuƙar ɓace tace, "don kutmar kan ubanki waye suke rayuwar ƴan wahalar? Bari in bambance miki rayuwar ƙauye da Birni." Kafin ka ce me; faɗa ya kaure an kasa ɓanɓare hannun Maryamu a jikin Mubeena don ba ƙaramin shaƙa tayi mata ba, Sai zage-zage take yi tana dukan duk wanda ya taho ƙwatan Mubeena a hannunta Ai da gudu sauran suka je suka kirawo su Aunty Salma, nan da nan aka cika ɗakin daƙyar aka ƙwace Maryamu har lokacin zage-zage take yi a cewar ta, "a barta ta ci kan uwarta." Aunty Salma da ranta ya ɓaci itama tace, "don ubanki ta fi ƙarfin ki ci kan uwarta, don Ni uwarta sai dai a mayar da ke ƙauyenku da ƙasusuwa a karye. Dama tun farko yarinyar nan ina da cikin ta wlh, to yanzu zan yi miki dukan tsiya in ga uban da ya tsaya miki, mu ba Sa'an yin ki bane." "Haba don Allah aunty Salma, ke da za ki raba su mene ne kuma na zage-zagen nan? Kin san abun da ya haɗa su ne?" In ji Aunty Zainab tana janye Maryamu da ke ta faman haki tana muzurai tamkar wacce iskokanta suka tashi Su Momy ne suka shigo a lokacin don suma yanzu labarin yakai musu ana faɗan, a tare suka shigo da Aunty Najwa suka ji Aunty Salma tana maganganun tana zagin Maryamu Aunty Najwa tace, "wai maimakon ki raba su shine kuma kika zauna kina zagin ta ita kadai? Wannan wanne irin abu ne?" "Nima abun da nake faɗa mata kenan." Rai a ɓace Aunty Salma tace, "eh dayake ba ƴaƴanku aka taɓa ba, ji be yanda ta shaƙe min ƴa tana son kashe min yarinya, to wlh bazan yarda ba idan ta kuma taɓa ta sai na ɗauki mataki a kanta nayi mata dukan tsiya a nan wurin." Momy riƙo hannun Maryamu tayi ganin har yanzu tana cika tana batse wa tana zazzare ido, hankalin ta ya soma tashi kar kuma a ce ciwon ta ne zai tashi, shiyasa tayi saurin jan ta suka fita batare da ta furta komai ba, tabar su nan suna ta cece-kuce, Kai tsaye sama ta haura da ita While Bintu itama tuni ta zame jiki ta je ta sanar da su Umman su abun da ke faruwa, But a cikin su babu wadda ta fito sun yi shiru suna jin hayaniyar ƙasa-ƙasa Su Asabe Matar Yaya Faisal su ne suka fice suka je wurin fadan, amma koda suka je babu Maryamun sai su Aunty Zainab suke ta maganar, Aunty Salma na yi suna tanka ta suna gaya mata, "abun da tayi bai dace ba, ai kamata yayi ta tsaya ta ji ba'asin maganar." Lokacin da Ammee ta zo wurin ne ma su Aakifah suke gaya mata dalilin faɗan, Ai kuwa buɗan bakin ta tace, "to ai kuwa maganar gaskiya ce tunda Maryam da auren SHAREEF a kanta, kuma Insha Allahu gobe uwar haka za a kaita ɗakin Mijinta, wannan taron da ku ka gani har da tariyan ta za a yi." Ai kuwa jin magana ta fito da gaske ne, sai fa rikici ya ƙara ɓarke wa, su Aunty Salma da su Aunty Hidaya waɗanda suka haɗa ƴan uba da su Momy, maganar ta sosa musu rai, a cewar su, "tunda ba a ɗauke su a bakin komai ba, ai ba a faɗa musu ba sai yau ake nuna musu basu da matsayi." Surutu dai kala-kala abun kamar zai zamar musu faɗa da su aunty Najwa Momy a lokacin ta baro Maryamu a ɗakinta ta zo tana basu haƙuri, amma inaa; maganar dai ta ƙi mutuwa, duk yanda ta so ta basu hujjar da zata kare kansu amma sun ƙi fahimta sai yaɓa maganganu suke yi, Shiyasa ta tafi tabar su nan, tabar su da su Aunty Zainab su faɗa; su faɗa, tunda ba baki suka fi su ba Magana dai sai da Dady ya zo ya tsawatar musu sannan ya faɗa musu dalilin ƙin bayyana musu maganar, yace, "shi da kansa yace kar a faɗa tunda ba tarewa zata yi ba, amma yanzu tunda dalilin tarewan ya zo dole zasu bayyana musu, don haka biki dai dana SHAREEF za a yi." Daga baya dai haka suka koma suna ƙus-ƙus babu kalan zage-zagen da basu yi ba, Abun da biyu ne dama tunda sun so su Hanif su auri ƴaƴansu, amma babu wanda ya neme su, sai wacce suke ganin ba kowa ba ita ce aka haɗa auren ta da SHAREEF, ai ga Mubeena ga sauran ƴan Matan da suke da burin haɗa auren zumunci, duk Momy ta ƙi basu fuska, Abun yayi musu ciwo sai dai haka nan suka liƙe maganar a ransu suka bar abun na ciki na ciki Yayinda Maryamu tana can ɗakin Momy, ta zaunar da ita tace, "kar ta fara ta fito." A tunanin ta ma ciwon ta ne ya tashi ko aljanun ta sun hayo, amma ganin yanda Maryamun ta ci gaba da harkokin gabanta da hankalin ta a jikinta, shiyasa hankalin Momy ya kwanta ta sake fita tabar ta a ɗakin, Sai da Dady ya dawo sannan ta jawo hannunta suka je ɗakin sa tunda yace ta kira ta Sai a lokacin Maryamu tasan mai ke faruwa tunda Dady yayi mata bayanin komai a yanzu, hankalin ta ya tashi tunda a yanzu gaskiya ba ta son SHAREEF sabida halayyarsa da yake gwada mata mugunta babu tausayi a ransa, a ganinta yanzu shi ba Mijin aure bane, ya fice mata a rai, Don haka ta buɗe baki tace, "Dady wlh ba ya sona, nima yanzu na haƙura dashi wlh, gwara a raba auren kawai." "A raba auren kuma Daughter?" Dady ya tambaya cike da mamakin furucin ta Yayinda Momy da ke tsaye tana sauraron su, sai ta koma ta zauna tana cewa, "zancen a raba ai bata taso ba Maryam, ko kin manta halin da kika shiga ne a kan soyayyarsa? Yanzu kuma shi da kanshi yace zai zauna da ke sannan kuma ki ce a raba? Bayan kina ganin yanda mutane suka soma gutsiri-tsoma a kan maganar har hakan ya ja ku da faɗa, ai wannan hanyar ne kaɗai za ki bi domin tusa musu haushi, zuwan iyayenki ma sun zo ne har da tariyan ki, suna farin ciki kuma ki watsa musu ƙasa a ido?" "Momy..." "A'a ya isa, na san abun da za ki ce, a kan dai maganar ba ya sonki ne, to yanzu ke kike da damar da za ki ƙwace SHAREEF tunda har ya nuna zai zauna da ke, ita wancan da kike tunani a kanta tana can inda ta fi wayau ta ƙi amincewa ta zauna da shi, don haka wannan damar ki ce Maryam, ba na son wata zance da zai fito a bakin ki; ki shirya gobe ke ma za a kaiki dakin ki, maganar makarantar ki kuma; mun rigada mun yanke hukuncin daga baya za ki zana jarabawar Weac da Neco sai ki fara babban makaranta, kin san dai da muna so mu raba auren nan da tuni mun raba shi, sabida halin da kika shiga a baya da kuma abubuwan da SHAREEF yayi miki, to ki yi hakuri kawai baza a raba auren nan ba, dama burinmu kenan ki samu wani matsayi a wurin sa, kuma yanzu kin samu tunda ya amince da ke." Kallon Momyn kawai Maryamu take yi idanunta sun cika da hawaye, gani take yi kamar har da son kai a maganar Momyn, tunda ita yanzu ta nuna ba ta so why not baza a raba auren ba, mutumin da ya nuna ba ya sonta don yanzu yace zai zauna da ita; hakan kuma sai su goyi bayan shi, Kallon Momyn kawai take yi tana sauraron ta zuciyarta na mata zafi Dady yace, "haƙuri za ki yi Maryam babu zancen raba auren nan, mun san kina sonshi kuma babu yanda za a yi ki dena sonshi tunda tun farko kin furta, na san ɓacin rai ne da kuma abubuwan da yayi miki a baya, amma mu muna alfahari da wannan auren daughter, za ki ji daɗin sa Insha Allahu Allah zai sanya muku albarka a auren nan, don haka ki yi biyayya kinji ko kamar yanda tun farko kika yi mana, SHAREEF bazai taɓa cutar da ke ba a wannan karon, idan ma ya cutar da ke ga ki gani ki zo ki sanar min zan ɗauki mataki." Ya ƙare maganar cikin lallaɓa ta ganin hawaye sun cika idanunta Maryamu ta kasa yin wata magana sabida sun ɗaure ta da jijiyoyin wuyanta, bata da yanda zata yi, idan ma ta bijire ga Iyayenta a gidan su zasu ji kunya, har ga Allah yanzu babu SHAREEF a ranta, amma ta san yanda zata dauki mataki a kansa, wlh wlh in har ta amsa sunan ta Maryamu sai ta ɗauki fansar wulaƙancin da SHAREEF yayi mata, don haka ta komar da hawayenta ta hana su fito wa, ta nuna musu ta amince da abun da suka ce Sun ji dad'in amsar ta, daga nan Dady ya sallame ta yace, "ta tafi zasu yi magana da Momyn nata." Tashi Maryamu tayi ta fita zuciyarta har lokacin tafarfasa take yi, ranta a ɓace yake, a fusace ta bi ta benen baya zata sauka, amma sai ta jiyo sautikan dararrakun su Halliru da Bashir, har da Sadiq don shima ya dawo bikin ne a yau, Suna zaune a kan benen suna ta hira har da wasu daga cikin Abokan Sadiq ɗin, Koma wa tayi da baya ta zo wuce wa ta bakin ƙofan su SHAREEF da ta wuce, yanzun ma har ta gibta sai kuma ta ga baza ta iya barin baƙin cikin da ke ranta ba, sai ta je ta gaya masa magana ko zata samu zuciyarta ta samu sauƙi, Tura ƙofan tayi da ƙarfi ta shige tana bin ko'ina da kallo; kasancewar akwai duhu babu hasken glop, hannu ta saka ta laluba ta kunna glop ɗin sannan ta soma duban Falon, ganin babu kowa sai ta nufi kanta tsaye cikin bedroom ɗin; nan kuma ta kwankwasa tana son ta ji ko akwai motsin mutum Daga ciki SHAREEF ne kwance a saman gado ya gama sharan barci, tashin sa daga barcin kenan sai dai yana a kan gadon bai miƙe ba idanunsa a rufe, ya soma jin sautin nocking, a hankali ya buɗe madaidaitan idanuwansa masu cike da barci yana sakin hamma, Jin ana sake buga wa ne, sai yace, "Yes." Yana ƙoƙarin tashi zaune, Ɗakyar ya miƙe ya zauna a bakin gadon amma ya kasa tashi Itama kuma Maryamu tana jin muryansa sai ta ƙara buga ƙofan da ƙarfi; sabida bata gane muryan waye ba, ba ta son ta shiga ciki kuma ba SHAREEF bane "Wai waye ne?" Yayi maganar da ɗan ƙarfi yana miƙe wa da nufan wurin ƙofan Yanzu ta gane muryansa shiyasa ta tura ƙofan ta shiga suka kusa cin karo a bakin ƙofan, Saurin ja da baya tayi gabanta na faɗuwa sabida ganinsa babu kaya daga shi sai short wando Da tsananin mamaki shi kuma yake kallonta bai iya cewa komai ba illa bin ta da ido da yayi kamar zai cinye ta, yana ƙare wa jikinta kallo Tana sanye cikin doguwar rigan material blue colour mai design na flowers an ƙawata shi da kalan ja da fatsi-fatsin brown, yayi mata cif ƙirjin nan nata kamar zasu faso a cikin rigan, farin hula ne a kanta na sanyi amma yayi baya kamar zai cire, wanda hakan ne yasa gashin gaban kanta ya bayyana Almajiran gashin kanta sun fito waje, manyan idanuwanta sun ɗan yi ja sakamakon ɓacin ran da take ciki da kuma hawayen da ke tattare a cikin su sun kwanta suna shirin fitowa Maryamu duk tadabarbarce sabida ganinsa ƙiƙam babu kaya a jikinsa, tana kallon tsarin jikinsa da ke cike da gashi gazar-gazar musamman ƙirjinsa yayi luf sai sheƙi yake yi, shiyasa lokaci ɗaya ta janye idanuwanta tunda tayi masa duba ɗaya, ta ja da baya tana kama ƙofan tare da ƙoƙarin daidaita kanta Shi kuma yana tsaye ya zuba mata ido kamar zai cinye ta, idanunsa ƙyam a kan ƙirjinta ko ƙoƙarin ɗauke su ba ya yi Ɗagowan da zata yi ta ga kallon da yake mata, hakan ne ya ƙara fusata ta bata san sanda wani jarumta ya zo mata ba; ta kalle sa rai a ɓace tace, "mene ne dalilin ka na son zama dani har ka iya canza ra'ayi a kaina? Ko har ka manta abubuwan da ka faɗa a kaina ne maganganun ka da baza su taɓa gushe wa a ƙwaƙwalwa ta ba?" Ɗan waro idanu yayi waje yana mayar da su cikin nata, kamar zai yi magana kuma sai ya kama haɓa yana ci gaba da zare mata idanunsa; alamun har yanzu mamakin ta yake yi Ita kuma Maryamu ranta ya ƙara ɓaci, cikin fushi da wani irin haushin sa tace, "ko don kana ganin na zama Mutum shine don baka da kunya har kake iya tunanin zaka same Ni a banza a hofi? Wlh bari ka ji Ni Maryamu ba na tsoron ka kuma duk abun da ke raina sai na faɗa maka shi, tun wuri ka je ka janye maganarka kar kayi gigin da zaka ce zaka ɗauke Ni ka kaini gidan ka, kai ka gaya min wannan maganar a baya, amma yanzu Ni ce zan faɗa maka, idan ka sake kayi kuskuren da na sanya ƙafata a cikin gidan ka." Sai ta kaɗa baki tana sake ware manyan idanuwanta da suka sake yin ja, "Zan nuna maka ainihin wace ce Ni, kuma ƴar ƙauyen nan dai da ka raina." Ta ja dogon tsaki ta juya zata bar Falon babu ko tsoron sa a cikin ranta But bata san yana biye da ita ba, sai ji tayi an fizgo ta baya tayi shirin faɗuwa, da hannu ɗaya ya riƙe ta ta tsaya a kan ƙafafuwanta, yayinda yake sauke mata wani kallo mai wuyan fassara fuskarsa babu annuri ko kaɗan. _Fatan an yi azumi lafiya? Allah ya nuna mana na wani lokacin lafiya yasa muna da tsawon kwana, a yi sallah lafiya Masoyana._ 20/April/2023. Eid dul-fitr. [23/04, 5:29 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* _Ina barar addu'a daga bakunan ku Masoyana, zan zana Final exam ɗina, ina roƙon Allah ya bamu Sa'a ku sa mu a addu'a. Nagode._ __________ *BOOK2* _______________*PAGE23* _____Saka hannu ya kuma yi ya janyo ta zuwa jikinsa ya haɗe su wuri ɗaya, yayinda ya ɗaura hannunsa a ƙugunta yayi mata riƙon da baza ta iya kufce wa ba, abun mamakin lokaci guda ya yalwata beauty face ɗin sa da wani killer smile wanda ya bayyana kyawawan dimples ɗin sa, idanunsa a kanta suke; in cool voice yake faɗin, "lallai kina da ƙarfin hali, I solute you." Ya ƙare maganar still da murmushin a kan fuskarsa yana bin ta da kallo ko ta ina Ƙoƙarin ƙwace wa take yi but ta gaza, ba ƙaramin shiga wani yanayi tayi ba da jin ƙugunsu a haɗe numfashin su na cakuɗuwa da juna, inda ƙamshin turaren sa tamkar ya fesa a yanzu ya cika mata hanci ta soma kokawa da nimfashin ta, duk yanda ta so ta ƙwace amma inaa; ta gaza, domin ba karamin riƙo yayi mata ba Da gayya yayi mata don ya ga iya gudun ruwan ta, har yanzu da murmushin nan a kan kyakkyawar fuskarsa, inda yake bin baby face ɗin ta da kallo ganin yanda ta haɗe ta kamar zata fashe don kumbura, "Realize Baby, ba gargaɗi kika zo min ba? Shine nace ƙarfin halin ki ya burge Ni, kar ki damu komai na ɗauka." A fusace kamar zata yi kuka tace, "wlh sai na rama duk wulaƙancin da kayi min, kuma ba na sonka a yanzu sabida kai mugu ne azzalumi wanda bai da ɓurɓushin imani a zuciya, na tsane ka bazan taɓa zama da mugu kamar ka ba, azzalumi..." Sai tayi shiru sabida kukan da ya taho mata, Dakyar ta riƙe shi amma idanunta sun sake kaɗa wa sosai sun tara ruwan hawaye tana aika mishi da muggan kallo idanuwanta kamar zasu tsiyaye a ƙasa Yayinda yayi kamar maganar nata bai taɓa shi ba, duk da babu wannan murmushin a kan fuskarsa, amma a sake take fuskar nasa, kuma sosai ya ƙara ƙanƙame ta yana sake manna ta a jikinsa, dukkan su nimfarfashi suke saki wanda ke dukan fuskokin juna, Musamman nata da ke fita da ƙarfi sabida yanda take a zuciye kamar zata shaƙe shi don haushin sa, Huro mata iska yayi a kan face, sai ya sake rage murya tare da kai bakinsa dai-dai kunnenta, bai yi maganar ba sai da ya haɗe bakinsa da kumatunta ya ɗan goga; idanunsa a lumshe yana amsar sabon yanayin da ke baƙuntan sa Jin ta janye fuskarta ta daka masa tsawa a kan, "ya sake ta." Dalilin da yasa ya buɗe idanun nasa kenan waɗanda suka soma sauya launi tsaban jarabar da ya soma fizgar sa, bakinsa ya sake haɗa wa da kunnenta dakyar ya furta, "yanzu ba na jin tsanar ki a raina shine dalilin da yasa zan zauna da ke a matsayin Matata, kuma har yanzu ina jin cewa kina sona a ranki, ban fita cikin zuciyarki ba." Sai yayi shiru na ɗan seconni before ya ƙara da faɗin, "bakin da ya furta SO... Ba ya sauya wa, ina ji a raina kina sona har yanzu, now damar ki ne kar ki cuci kanki da wannan haukan naki, ki bari mu ji daɗin rayuwarmu." Tuni ya mayar da kansa a saman wuyanta ya manne mata yana ƙoƙarin cusa kansa a ƙirjinta Wanda a lokacin ne ta samu damar ɓanɓare jikinta, kuma a dai-dai lokacin hawayenta suka soma gudun tsere sabida tsananin takaici da baƙin cikin abun da yake mata, ƙarfinta ta sanya ta ingije shi, yana sakin ta tayi bakin ƙofa da gudu, sai da ta buɗe ƙofan sannan ta tsaya tana duban sa, hawayenta na zuba a kan face ɗin ta cike da bakin ciki da tsanar sa tace, "har abada bazan sake nuna wa mutum mugu mara imani irin ka soyayya ba, domin ada nayi kuskuren zaɓan ka da har zuciyata ta makance a kanka, wlh na rantse da Allah sai kayi dana-sanin zama dani in har kayi kuskuren da aka kawo Ni gidan ka." Sai ta tofo mishi yawu kamar yanda ya taɓa yin mata, ta fice da gudu tabar wurin Duk da yawun bai taɓa shi ba, amma maganganun ta sun sosa mishi rai, ya jima yana tsaye a wurin kafin ya taka ya wuce cikin bedroom ya koma ya shiga toilet. Lallai yana jiran ranan da zata ɗauki fansa a kansa While Maryamu tana tafiya hawaye na tsiyayar mata bakin ciki da takaicin SHAREEF ya cika ta, wlh ta ɗaukar wa kanta alƙawarin sai ta rama abubuwan da yayi mata, sai ya raina kansa kamar yanda ya wulakanta ta itama, ta gode Allah da yanzu haushi da tsanar sa ke tasiri a zuciyarta, ta yanda zata rama duk abubuwan da yake mata, Kai tsaye ɗakin da aka sauke su Innarsu ta wuce, sabida duk wasu suna sallah gidan yayi shiru kamar babu jama'a a ciki, Koda ta shiga ɗakin da su Innar su suke ciki, suma sallan suke yi sai Yaron Bintu da aka ajiye a kan gado yana ta tsala kuka, Ita kuma Bintun tana cikin toilet tana alwala, Zuwa Maryamu tayi ta ɗauki Yaron duk da bata a yanayi mai daɗi, ta soma rarrashinsa sai ga Bintun ta fito, "Ashe kina ji don wulaƙanci Yaron na kuka kika bar shi?" Bintu da ke faman sharce ruwan fuskarta take cewa, "to don Allah zan ƙi yin Sallah ne? Kowa na sallah Ni kuma so yake yi ya hana Ni, don Allah ki riƙe min shi bari in yi sai in amshe shi." Banza Maryamu tayi mata tana ci gaba da rarrashin Yaron, but tunanin ta ba ya wurin gaba ɗaya Sai da Matar Yaya Ashiru ta soma idar da sallan, tace, "ta kawo shi ta riƙe shi, sai itama tayi sallan." Yaron ta miƙa mata before ta shiga toilet ɗin ta ɗaura alwala, tana fitowa ta yayimi Hijabi a kan gadon da bata san na waye ba, itama ta kabbara sallan, Lokacin da ta idar an rage yawa a ɗakin, Daga ita sai Innar su da har yanzu itama tana zaune tana lazimi Gefe can kuma Asabe ne da Matar Naziru suna zaune suna hira, ita kaɗai ce yanzu bata haihu ba don itama da ƙaton cikin ta Matar Yaya Ashiru kuma har yanzu shiru Allah bai bata cikin ba Ganin babu mutane sosai sai Maryamu ta matsa kusa da Innarta tana cewa, "Inna wai dama kuna da labarin zan tare shine dalilin ku na zuwa nan gaba ɗaya?" Kallonta tayi, sai kuma ta kawar da kanta tare da amsa mata tace, "muma dai daga baya muka ji labari, har nace bazan zo ba amma Yaya Ahmad ya roƙa in zo, ba don haka ba mai zai kawo Ni? Tunda ga Ummanku ai kamar na zo ne." Tura baki Maryamu tayi tana cewa, "nima Inna wlh tallahi na dena son auren nan, idan za a bi ta nawa a warware shi kawai." "Ta ya ya kenan?" "Ta inda aka haɗa shi ta nan za a warware shi." Wani kallo Inna ta watsa mata tace, "ke fa ba ki da hankali na kula, ashe duk zaman nan naki ba ki yi hankali ba kina nan da shirmen ki wato? Halin ki na nan na faɗa ace duk yawan mutanen da suka cika gidan nan sai da kika nuna halin ki; kika jajibo wata kuna faɗa tunda ba ki da hankali ko?" Zata yi magana Innan ta daka mata tsawa, "rufe min baki don ubanki, ki mayar da hankali ki ci gaba da abun da kike yi tunda ba ki san kin girma ba, shashashan yarinya, wa ya sani ma Allah kaɗai ya san abubuwan da kika yi musu tun zuwan ki garin nan, iskancin ki da kike yi a can ƙauye shine kika taho dashi har yanzu ba ki fasa wannan halin naki ba, to in kuma jin kin ja wata faɗa kinji ko? Wlh sai na miki dukan tsiya banzan yarinya." Tashi Maryamun tayi tabar ɗakin ranta a mugun ɓace, kai tsaye cikin ɗakin ta ta wuce ta tarar da su Aakifah suna zaune suna hira Ai kuwa suna ganin ta suka hau tsokanarta suna ce mata, "Amaryan Yaya SHAREEF Amaryan Yaya SHAREEF." "Wai ashe kin san da wannan maganar Maryam, but tun zaman mu ba ki taɓa faɗa mana ba?" A cewar Yusaira tana dariya Ita kuma Maryamu tayi banza da su sabida ranta a ɓace yake, shiyasa ta kasa biye musu tana jin su suna ta tsokanarta Sai da Bintu ta zo ta kira su a kan, "su zo su ci abinci in ji Momy." Sannan suka fita suka koma Falon da aka cika da mutane, kowa yana harkan gabansa, Abincin suka zuba su huɗu suka ci suna hira da raha, tuni sun sauya hiran nasu tunda sun ga Maryamu ba ta son wancan maganar, dalilin da yasa ta saki jiki kenan suka yi hiran tare Bayan sun koma daki kuma ta garƙame ƙofan tace, "wlh babu wata shegiya da zata sake shigo wa ɗakin nan, su je su nemi dakin kwana, don wlh idan yarinya tace zata kwana a nan sai na sumar da ita, sai dai uwarta ta haifi wata." Mai su Aakifah zasu yi ban da dariya, sai dariya suke mata tunda sun san da su Mubeena take yi, dayake a nan suke kwana, yau kuma ta rufe ƙofan, duk bugawan da aka yi basu buɗe ba, Su biyar suka kwana a ɗakin duk da Yaron Bintu A washe gari kuma aka tashi da biki gagarumi, Karfe sha ɗaya aka ɗaura auren Hanif da Amra Kayan da Maryamu ta saka duk Momy ta saka a ɗinka mata, duk da a ƙurarren lokaci ne amma kasancewar akwai kuɗi nan da nan aka samu ɗinkunan, da safen ranan bikin aka kawo su kusan kala biyar, Haka ta dinga saka wannan ta fita wannan dolen ta tunda su Aunty Najwa ne masu shirya ta, Har makeup ɗin nan na zamani aka yi mata sai ɗaukar pictures ake yi kala-kala da su Momy, Itama Maryamu saboda ta ba ire-iren su Aunty Salma haushi waɗanda kallo ɗaya kayi musu zaka ga rashin walwalan su a fili, shiyasa ta saki jikinta tana ta farin ciki komai aka ce tayi sai tayi shi, sabida har a ranta ta ɗauki ɗammaran babu sauran nuna baƙin ciki bare har ta shiga damuwa a kan auren nan, yanda ta shirya wa zuciyarta na ɗaukar fansar abubuwan da SHAREEF yayi mata, Hmm kawai Allah-Allah take yi a kaita ta soma abun da ta ƙulla Ƙarfe daya bayan an yi sallan azahar, wasu suka ragu suka tafi gidan Maryamun, har da su Inna waɗanda zasu ga gidan kamar yanda Dady yace, "su je su duba komai su saka albarka." Bayan sun tafi ne aka kira masu kiɗan ƙoroso mata suka yi ta cashe wa Da wuri-wuri aka shirya tafiya da Maryamu, bayan su Inna sun dawo aka kaita har wurin su suka yi mata nasiha, Umma ce kawai tayi mata faɗa amma Inna bata ce komai ba sai fatan zaman lafiya da tayi musu, Haka aka zagaya da ita wurin dangin Momy suka yi nasu daga ƙarshe aka kaita ɗakin Dady tunda yana gidan, Sun jima yana mata nasiha sosai before aka fito da ita, Kaf ƴan Matan sai da suka bi ƴan kai Amarya, domin su Aakifah su ne gaba-gaba, Har aka fice Maryamu babu ɗigon kuka ko na kewa a kan fuskarta, Haka aka tafi da ita gidan ta da ya haɗu sosai Dady yayi aiki ba kaɗan ba, Anguwa daya suke da gidan Hanif, sai dai akwai tazaran tafiya don ba kusa bane gaskiya, Kuma daga Maryamun har Amra shi yayi musu kayan ɗaki, set ɗin kujeru har biyu, gaskiya gidajen yayi musu na gata ne Su Mubeena da suka je don ganin ƙwaƙwaf, haushi kamar ya kashe su, haka suka yi ta zagaya gidan suna kallon abun haushi, Basu baro gidan ba har bayan magriba sannan aka zo aka tarkata su gaba ɗaya, sabida ba a son a kwanan mata tunda yanzu an dena wannan yayin Aka bar Maryamu ita kaɗai babu ɗar bare damuwa don an tafi an barta, tana ganin ma kowa ya watse ta rufe ƙofan ɗakinta ta murza mishi key, Ta ɗauki wayanta ta soma latse-latse, daga nan bata sake jin motsi ba har tayi barci kuwa.*** Shima SHAREEF shi kaɗai ya shigo gidan, don ya ƙi yarda Abokansu su rako su sai dai suka bi Hanif gidan sa, Kai tsaye ɗakin sa ya nema ya shiga, dayake ɗakuna biyu aka saka gado, yana duba wa ya ga mai furnitures ya shiga ciki, A daren ya kira Sadiq ya kwaso masa wasu daga cikin kayan sa ya kawo masa, Yana tafiya yayi wanka ya saka kayan barci, har ya fita ya duba ɗakin da Maryamu take ciki, ganin a kulle tunda ya taɓa sau ɗaya sai ya juya ya koma ɗakin sa yayi kwanciyar sa, tunda akwai gajiya a jikinsa shima nan da nan barcin ya ɗauke sa, yana mai cike da mafarkan yanda komai ya sauya mishi da kuma yanda zasu zauna da Maryamu. *** _____Washe gari wurin ƙarfe sha ɗaya su Aakifah suka sake zuwa gidan, har da su Ammee Suna tafiya shima Hanif yakai Amra gidan su, Dayake Momy tace mishi, "ya kawo ta su Inna zasu tafi zasu ganta." Tunda lokacin har sun shirya jira kawai suke yi su ga Amra sannan su tafi, har sun yi sallama da Dady ya sallame su da alkhairai mai yawa, Motan da zata tafi dasu ma tana cikin gidan an kawo ta, Bayan sun ga Amran sun sanya mata albarka sannan suka tarkata suka tafi Sai gidan ya zama daga Momy sai Amra da Hanif ɗin, Don shima zaman sa yayi suna ta hira da Momy, Amra kuma na zaune a ƙasa tana sauraron su, idan sun yi abun dariya ta murmusa fuskarta rufe cikin Hijabin ta Sai kusan sallan la'asar su Aunty Hidayat suka dawo gidan, Shiyasa Momy tace, "in zasu wuce kawai su tafi da Amra gidan su; su Hajiya su ganta." Tunda babu wacce ta zo bikin, tsufa ya hana su fita ba ko'ina suke zuwa ba Bayan sun yi Sallah sai suka tafi haraban gidan, Momy ce ta riƙo hannun Amran ta sanya ta a Motan da su Mubeena suka shiga Bayan sun tafi sai ta koma ciki tace ma Hanif, "idan anjima yayi sai ya je ya ɗauko ta su wuce gida. Kar ya ƙara kawo ta har ta saba da gidan ta tukun zasu sake fita." Shi dai Hanif dariya kawai yayi, yana zaune suna ta hira, sun jima tare sai da su Aunty Fatima suka dawo gidan sannan ya fita zuwa haraban gidan yana waya da SHAREEF, Tsokanarsa yake yi yana cewa, "ya ba shi labarin daren su na jiya, Allah yasa dai yana cikin farin ciki komai ya wakana?" Tsaki SHAREEF yayi yace, "kai fa banza ne, ba na son irin haka wlh." Dariya Hanif yayi yana shafa ƙeya yace, "to mene ne a ciki? Kawai fa tambaya nayi." Tsakin ya kuma ja yace, "to babu abun da ya faru don ubanka." "Lallai, to mai ka tsaya yi? Kai da kake jiran wannan ranan Bro? Yakamata dai a haɓɓaka sunna don Ni tuni na wuce wurin, ka ga sai Matanmu su haihu a lokaci ɗaya wlh, mu saka musu Hassana da Hussaina, ko Hassan da Hussain. Allah ina baka shawara Bro yanzu komai ya wuce damar ka ne, ka daure kayi abun da yakamata." Shiru SHAREEF yayi masa yana ta zuba, har sai da ya gaji ya kashe wayan sa yana jan tsaki, Sai dai a ransa shima yana jin bazai iya ɗaukan lokaci mai tsayi bai je ga Maryamu ba, don haka shima dole ya angwance a wannan ranan, Yana ɗakin sa a wannan lokacin ya rufe kansa, duk hayaniyar da su Ammee suka yi kafin su tafi yana ji, sai da suka bar gidan sannan ya fita yayi sallan la'asar, already azahar a cikin ɗakin yayi don ba ya son ya fita su gansa, Bai sake fita ba sai da aka kira magriba sannan ya fito, Motocinsa guda biyu suna nan a fake a gidan kasancewar Sadiq ya kawo mishi, Fita yayi ya nufi masallacin anguwan yayi Sallah, bayan ya idar yayi zaman sa yana ta faman zikirori da addu'a, tunda a yanzu ya yi wa kansa faɗa sosai, musamman tun sanda ya sauya ya soma addu'a yana roƙon Allah a kan soyayyar Haseena, ya ji dama-dama a yanzu babu ƙuncin da ke tare da shi, duk damuwar da yake yi da ita ya ragu sosai, dalilin da yasa ya ƙara natsuwa kenan ya kama Allah a yanzu ya dena wasa da Sallah ana kira yake yi a kan lokaci, in har ba wani abun yake yi mai muhimmanci ba; ba ya barin lokaci ya ƙure mishi, to Alhamdulillah ya ga sauyi sosai, Koda ya fito daga Masallacin; har ya shiga gida kuma sai ya ɗauki Mota ya fita, inda suka tsaya a daren jiya Hanif yayi siyayyan Kazan shi, a nan shima ya faka ya siya yau, tunda a jiyan ya ƙi siya kamar yanda Hanif da su Habib suka takura masa, amma yayi banza da su ya ƙi siya a haka suka bar wurin Bayan ya gama siyayyan ya wuce wani shago ya siya drinks sannan ya nufo gida, Sai da ya rufe gate ɗin sannan ya shiga cikin gidan riƙe da ledojin a hannunsa, yana shiga Falon nan ma ya garƙame ƙofan sannan ya juya ya nufi cikin Falon. [25/04, 7:17 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱 *SHAREEF* _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE24* _____Maryamu tuni ta gama shirin barcin ta; ta sanya sleeping dress riga da wando masu taushi kalan lemon green, ta ɗaura hulan zaren lilo baƙi a kanta, tana kwance tana latsa waya ta ji bugun ƙofa, Hakan ne yasa ta dakatar da abun da take yi tana duban wurin ƙofan, ta san dai bazai wuce SHAREEF bane tunda ta san su kaɗai ne a gidan, kuma tana jin fitan Motansa da dawowarsa, shiyasa ta ja dogon tsaki ta ƙi miƙe wa bare ta buɗe ƙofan, haushi da takaici ya cika ta; a ranta tana tunanin abun da zai yi mata har yake iya buga mata ƙofa, Jin ya ƙi dena wa sai ta miƙe a fusace ta nufi ƙofan, tsaya wa tayi a wurin ta ɗaga murya tana cewa, "wai waye ne?" Shiru SHAREEF yayi kamar bazai yi magana ba, sai kuma yace, "ki buɗe ki ga waye." "Bani da lokacin ka, mene ne kake buga min ƙofa ka hana Ni saƙat bare nayi barci?" "Ki buɗe sai ki ga mene ne." A tsiwace tace, "bazan buɗe ba, ka ga; na fa san mai kake biɗa a wurina, to bari ka ji duk maitan ka da nacin ka wlh baka isa ka samu abun da kake so ba, domin Ni Maryamu na fi ƙarfin ka sai gani sai hange, kabar ganin an kawo Ni cikin gidan ka kayi tunanin zaka mayar da Ni abun biyan buƙatarka tunda ban san abun da nake yi ba, to ka cire tunanin nan a ranka har abada baza ka taɓa samun abun da kake so ba, kai baka ji kunya bama? Wacce ka tsana kake ƙyamata kashi ma ya fi ta a wurin ka; amma don rashin imani da rashin tausayi ka zo nan domin neman buƙatar ka." "Ni kike fada wa wadannan maganganun?" "Eh an fada maka, in na fito ka yanka Ni." Ta ja tsaki tabar wurin tana koma wa kan gadonta ta kwanta, har da harɗe ƙafafu Yayinda SHAREEF kuma ajiye ledan yayi a wurin ya juya ya koma ɗakin sa, lallai zai yi maganin bakin rashin kunyar yarinyar nan, bazai iya jure rashin mutuncin ta ba, ransa ya ɓaci haka ya dinga zagaye a ɗakin sa, amma daga baya sai ya taushi kansa yana zama gefen gadon, yayinda ya kama kansa abun duniya ya ishe sa yayi masa yawa, har ga Allah bazai iya haƙura da Maryamu ba, yana matuƙar buƙatarta a rayuwa, kome ta faɗa mishi ya san shi ya jawo, amma bazai iya jure rashin kunyarta ba, shima dole ya tashi tsaye ya nuna mata halin sa ko don ya saita mata kanta, Daƙyar ya samu yayi barci, sai da ya kuma zuba ruwa a jikinsa sannan ya ɗan ji dama-dama, ya afa maganin sa sannan ya kwanta, ya jima yana juye-juye before barci ɓarawo ya sure sa cike da mafarkan Maryamu, Bai tashi ba sai asuba, dole yayi wanka yayi alwala ya sauya riga ya tafi masallaci, Bayan an idar da sallan ya dawo ɗakinsa, yana cire rigansa ya koma wani barcin Itama Maryamu barcin ta koma tun Sallan asuba, sai karfe bakwai ta tashi, ta jima a zaune before ta shiga toilet tayi uzurin ta ta fito, sannan ta gyara ɗakin nata ta wuce Falo, dayake zaman su a Abuja ta saba da aiki, da asuba ba sa koma wa barci ma zasu Fara aiki, duk da yanzu sabon gida ne amma hakan bai sa ta ƙi kakkaɓe Falon ba, duk ta jera pillown kujerun tayi style da su, Wurin ledan da ya ajiye mata a bakin ƙofa ta nufa ta ɗauka ta duba abun ciki, taɓe baki tayi tana hararan ƙofan ɗakin sa, sai ta ja guntun tsaki a fili tace, "wato shi ga shi mara kunya ya ɗibo jiki raɓe-raɓe zai zo wurina, Hmm lallai ne ma SHAREEF, yanzu na zama Mutum amfanina ya zo za a zo a more Ni a banza a hofi, wlh baza ka taɓa samun abun da kake so ba, mu zuba dani da kai." Ƙwafa tayi tana ɗaukar ledan ta wuce wurin freezern ta ƙato, dayake jiya an cika mata da ruwan Faro sai Lemon kwali da coke na robber, har sun yi sanyi tunda akwai nepa a gidan, su Ammee da suka kunna tun jiya ita kuma ta manta bata kashe ba a haka ya kwana, drinks ɗin ta kwashe ta zuba a ciki sannan ta wuce kitchen, a can ma an saka mata babban freezern duk da bai kai na falo ba Gaskiya Dady ba ƙaramin ƙoƙari yayi ba, komai shi yayi musu na kayan furnitures tunda shi ya bada kuɗi aka siya, a kayan akwati ne kawai Momy ta bada nata gudunmawar, duk abubuwan da ta san zata bukata an zuba mata a akwati musamman ƙananun kaya da aka jibga mata kamar babu gobe Kazan ta gasa yayi ɗumi sannan ta tafasa ruwan zafi ta ɗauko flaks ɗin ta ta zuba a ciki, sai ta soya ƙwai ta ɗauka ta fita zuwa Falo, a saman dainng ta ajiye komai har plates; sannan ta zauna ta haɗa tea tana kora wa da ƙwan tunda babu bread, bayan ta gama ta soma yagan kazan, sai da tayi mishi cin mahaukata ta kusa take rabin kazan sannan ta hakura saboda yanda cikin ta ya cika fam kamar zai fashe, gyatsa tayi ta furta Alhamdulillah tana lanɗe baki, an samu na banza. miƙe wa tayi ta wuce ɗakin ta, wanka tayi ta fito ta zauna a gaban mirror ta caɓa kwalliya, sannan ta nufi akwatunan ta tayi ɗaiɗai dasu har sai da ta ɗauko kayan da ya dace da ita, After ta saka ta koma bakin mirror tana kallon kanta, Dariya ta fashe dashi tana tafa hannaye, Ba ƙaramin kyau ta yi wa kanta ba don ta kasa rufe baki a yadda ta ga haɗuwar ta, Ƙananun kaya ne riga da wando kalan ruwan powder, gajeren wando ne iya cinyanta wanda ya matse ta tam ya fitar mata da lingu da saƙo na mazaunan ta, dama ga shi wandon robber ne tamkar an halitta shi a jikinta tsaban yanda ya kama ta hips din ta suka bayyana, sai gajeriyan rigan wadda iya cibiyarta ta tsaya ana kallon cibinta a waje, sai dai rigan ita kuma a sake take bata kama ta ba kuma tana da gajeren hannu ne, gaban rigan a buɗe take da kwalliyar stones masu ƙyalƙyali, iya saman ƙirjin ta rigan ta matse wanda ya bayyana mata breasts ɗin ta fili sun cika fam gunun sha'awa, ko bra bata sanya ba, Ga makeup ɗin da tayi laɓɓan nan sai glowing suke yi idanunta suna shining sun sha tozali sun yi haske, Sai juya wa take yi a gaban mirrorn tana ɓaɓɓaka dariya, Koma wa tayi ta ɗauko hula ta rufe cushin gashin ta da ta kasa gyara wa, illa oil mai ƙamshi da ta sanya mishi, ta ɗaura hulan turban kalan ja, ta ɗauki flat shoes shima ja ta sanya a ƙafafuwan ta, gaban mirrorn ta sake koma wa tana jujjuya jikinta, ba ƙaramin kyau tayi ba kayan suka haska ta tunda suna da haske, sun yi wa Black skin ɗin ta mugun kyau, Sai ta cije laɓɓa tana kaɗa kanta, "Hmm lokacina ne yanzu." Kama ƙugu tayi ta sake juya wa before ta ɗauki turaruka ta feffesa kala-kala, nan da nan ta ɗauki ƙamshi mai daɗi babu inda ba ya tashin ƙamshi a jikinta, Wayanta ta dauka ta fita Falo tana zama a kan sofa tare da harɗe ƙafafu A dai-dai wannan lokacin SHAREEF shima ya fito yunwa ya koro shi; yana tafe yana hamma, but babu inda idanuwansa suka sauka sai a kan Maryamu, take ya tsayar da bakin nasa a buɗe ya yatsa cak a wurin ya kasa gaba bare baya, Idanunsa sosai ya sake ware wa a kanta yana tunanin ita ce ko wata ce daban, domin har ga Allah bai taɓa tsammanin tsantsan kyawun halittarta ya kai haka ba har sai da ya ganta tamkar tsirara a gabansa; tayi irin wannan shigan da yayi mugu-mugun tafiya da duk wani imaninsa gami da natsuwar sa, zahiri shi kansa bai san sanda ya saki baki yana bin ta da kallo tamkar soko ba, yayinda ƙafafunsa tuni sun ɗibe sa ya tafi izuwa wurin ta, sai ganin sa tayi a gabanta a tsaye wanda bata san da zuwan nasa ba sai da ta hango ƙafafunsa; tunda kanta na ƙasa tana duba waya Take ta ɗago kanta ta zuba mishi manyan idanuwanta, nan da nan ta sha kunu ganin yanda ya zuba mata na mujiya yana kallon jikinta, dama da biyu tayi don ta nuna mishi ƴar ƙauye ta girma, dalilin da yasa tayi shigan kenan, wanda bata san cewa sabon rikici ta jawo ba Domin a lokacin ta gama rikirkita SHAREEF; ya gama fita a hayyacinsa, duk wani lungu na jikinsa tsuma yake yi gaba ɗaya ƙofofin gashin jikinsa masu sada mishi duk wasu saƙonni sun buɗe wutar tsananin sha'awa da bukatar kasancewar su tare ya tashi mishi, ga ƙamshin turaren ta da ya taimaka masa wurin dulmiyar dashi, kwata-kwata hankalinsa ba ya jikinsa idanunsa har sun soma kaɗa wa jikinsa na rawa ya kasa cire ido a kanta saboda gaba ɗaya hankalin sa ya tashi Ita kanta Maryamu ta soma ɗan ruɗe wa saboda ganin halin da yake ciki, har gabanta ya soma buga wa, amma sai tayi ta maza ta maze tana gyara zamanta tare da sake ɗaura ƙafa kan ɗaya Hakan sai ya ƙara bayyana manya-manyan cinyoyinta masu ɗaukar hankali a idanunsa, wanda tuni yayi ƙoƙarin kamo ta idanuwansa sun rufe burin sa kawai ya shaƙi ƙamshinta ya ji albarkatun jikinta cikin nasa Zumbur Maryamu ta miƙe sabida ganin ya yo kanta zai faɗa mata, idanunta ta ware waje kafin tayi ƙwaƙwƙwaran motsi ya cafko ta, Sai ganinta tayi cikin jikinshi ya ƙanƙame ta ya tusa mata kanta cikin ƙirjinsa; ya kasa bata damar ma motsa wa bare tayi wani motsi, sabida yanda ya matse ta ya ƙanƙame ta ƙam yana shaƙar ƙamshin turaren ta, Duk yanda ta so ta ƙwace amma inaa; ta gaza, domin ba ƙaramin riƙo yayi mata ba, Gaba ɗaya ta soma tsorata da halin da ya soma shiga sabida ganin yana shinshina ta yana ƙoƙarin lashe mata fuskarta da ya ɗago ya riƙe mata kumatu gam, Daƙyar ta iya furta, "meye haka kake yi? Dalla ka sake Ni, ba na so..." Saurin haɗe bakunansu yayi yana ƙanƙamo ta ƙam tamkar zai maida ta ciki, har wani ɗago ta yake yi, wani irin zuƙa yake mata kamar zai cinye ta, gaba ɗaya SHAREEF ya haukace ya rikice; ba ya iya gani ba ya ji a wannan lokacin, burinsa kawai ya samu abun da yake buƙata, tamkar mayunwacin Zaki haka ya koma farautan Maryamu wanda lokaci ɗaya ya soma galabaitar da ita, Kwata-kwata bai raga mata ba a yanda yake tsotse mata baki gaba ɗaya ya gama cije mata laɓɓa, domin da zafi-zafi yake kai mata sumba, Tsawon lokaci before ya dakatar yana zare bakinsa tare da mayar wa saman fuskarta ya fara lashe ta kamar wani maye, Inda hannayensa na zube a bayanta yana yamutsa ta har zuwa ƙasan mazaunan ta Ita kanta Maryamu ta soma fita a hayyacinta, domin jin waɗannan zazzafan saƙonnin sun soma mantar da ita da wanda take tare Nishi kawai suke fitarwa gaba ɗayansu wanda tuni ƙafafuwansu sun gaza daukar gangar jikinsu, Tuni sun zame ƙasa sai ga su malale a saman shimfiɗaɗɗiyar carpet din tsakar Falon Tuni SHAREEF ya soma ƙoƙarin ɓarka mata gaban riga, don yanda ya cafko breasts ɗin ta sai da ya fitar dasu daga cikin rigan, Nan fa ya fara mata wani irin salo mai sake rikirkitar da ita, Nan da nan ya ci galaban da ta soma biye mishi don tuni itama ta fita a hayyacinta, Sam a wannan lokacin babu mai ji bare gani sun shiga wani irin yanayin da sun manta gaba ɗaya kansu, Daɗin da suke ji yana ƙara ratsa musu kwanya yana sake haukata su da fitar da su a cikin hayyacinsu Tsawon lokaci suna wannan yanayin wanda ba ƙaramin galabaitar da Maryamu ya soma yi ba, Don abubuwan da yake mata hankalinta ya gaza dauka abun ya wuce tunaninta, Tun tana iya enjoyed abun har takai ga ta soma tsorata sabida yanda SHAREEF yake sarrafa ta da zafin shi babu ragowa bare sarara mata, Nan fa ta soma dawowa cikin hayyacinta; domin har ya soma ƙoƙarin zare mata wandon ta, Da sauri ta kama wandon cikin tashin hankali tana girgiza masa kanta, domin a wannan lokacin baza ta iya magana ba "Please ki bar Ni kar ki hana Ni, kar ki hana Ni zan mutu, don Allah ki taimaka min." Abun da ya iya furta wa kenan kamar zai yi kuka yana shige mata tare da tusa kansa a ƙirjinta yana fitar da numfarfashi, Hannunsa ɗaya yana saman wandonta yana ƙoƙarin cire mata shi dole Amma Maryamu ta ƙi yarda, domin a wannan lokacin abubuwan da ya dinga mata suka soma dawowa cikin kunnuwan ta, sam SHAREEF ba abun a tausaya mishi bane, domin shima bai tausaya mata ba, ba ta shigo cikin gidan sa bane don ya same ta da sauƙi har haka ba, dole sai ta nuna mishi muhimmancin ta baza ta taɓa amince wa dashi ba sai ta sa yayi nadamar duk abubuwan da yayi mata, sai ya durƙusa a gabanta ya bata haƙuri sannan zata iya yafe mishi, ya cutar da ita ba kaɗan ba, wanda yasa take a nan hawaye suka soma zubo mata, jikinta ya soma rawa haka ma laɓɓanta da take ƙoƙarin yin magana amma ta kasa, Tana son ta cire sa a jikinta amma ta kasa sabida ƙarfin ta ya gaza, shi kuma ya zame mata kamar maye tamkar ma kuzarin sa ne ya dawo fiye da na baya, Ganin yana ƙoƙarin afka mata da ƙarfi da yaji don ya zare wandon nata saura pant, Kuka ta fasa bata da wani zaɓi illa ta haukace masa nan take, Lokaci guda ta fara ihu da bige-bige tana yakushin sa iya ƙarfin ta Wanda tuni SHAREEF ya soma dawowa tunaninsa, domin yanda ya ga Maryamu ta haukace masa tana ihu da kururuwa, tana kai mishi duka ta ko'ina; azaban da yake ratsa shi tuni ya dawo hayyacinsa don har tulin gashin sa ta kama tana jan masa kamar zata tumɓuke mishi, Da sauri ya soma ƙoƙarin ɗaga ta don gani yake yi kamar zata iya kashe sa, Abun ya soma ba shi tsoro sabida ganin sosai take zabga uban ihu tana birgima kamar ba a cikin hayyacinta take ba, Baya ya ja jikinsa na rawa hankalinsa a matukar tashe, don tsab ya gane Aljanunta ne suka tashi, Ba karamin tsorata SHAREEF yayi a wannan lokacin ba, domin a yanda ya ga ta haukace ihunta yana ƙaruwa abun ya tsorata shi ba kaɗan ba, Saurin miƙe wa yayi ya rasa abun yi sai dube-dube yake yi, Da sauri kuma ya nufi hanyar kitchen ya je ya dawo batare da ya ɗauko komai ba, a yanda ya tsorata da halin da take ciki har jikinsa babu inda ba ya rawa, nan da nan ya haɗa gumi duk da babu kaya a jikinsa daga shi sai guntun wando, tunɓur-tunɓur haka yake yawo ya je nan ya je can ya rasa abun yi Wanda Maryamu na kwance itama babu kayan daga pant sai hulan kanta da bai cire ba, a yanda take haukan da fitar da ƙara zaka ce gaske ne, nan kuwa tsab hankalin ta a jikinta yake, Tana sane ta haukace tayi tamkar Aljanu ne a kanta sabida ta samu ta tsira, Duk abun nan da take yi tana ganin yanda SHAREEF ya rikice yakai ya dawo yana yawo tuɓur-tuɓur, hakan ba ƙaramin bata dariya ya so yi ba, amma sai ta maze ta ci gaba da ihun har da kiran, "wayyo Allah Inna, wayyo ki zo ki taimake Ni zai kashe Ni, wlh zai kashe Ni, ga shi nan, ga shi nan." Ta soma nuna inda SHAREEF ɗin ke tsaye yana fitar da gumi Da sauri ya tsayar da tafiyar da yake yi yana juya wa gare ta, a rikice yace, "ki yi haƙuri bazan sake ba, Ni ne? Ni ne ko? Na daina bazan sake ba. Don Allah ki yi hakuri. stop... Stop cry." Ya rikice ma bai san mai yake furta wa ba, Sai kuma ya juya da gudu ya nufi fridge ya ɗauko ruwa, Zuwa wurin ta yayi ganin ta soma rage ihun, Yana tsaye a ɗan nesa da ita yana tunanin abun da zai yi mata, Shi ba addu'a ya iya sosai ba balle yayi mata ta warke, Amma haka nan kuma ya bude ruwan ya zuba a hannunsa, yana ƙoƙarin tofa addu'a cikin hannun, Wai a hakan ne zai yi addu'ar a cikin ruwan, Amma ruwan tuni ya zirare ya zube Dariya ya so ƙwace wa Maryamu, sai kuma ta koma ci gaba da birgima ta je nan ta je can Da gudu ya koma ya sake ɗauko cup ya dawo, jikinsa sai rawa yake yi haka yayi ta maza ya tofa addu'o'in a cikin ruwan ya watsa mata Daga nan ne Maryamu ta soma barin abun da take yi, ihun ma ta dena ta koma sauke numfashin azaba, don ita kanta ta gwagwatu; duk ta gama ƙwale kai, Shiru tayi ta rufe idanunta tayi kamar mai barci Sai lokacin fa SHAREEF ya ji sauƙi a ransa, ya durƙushe ƙasa yana faman sauke numfashi hannunsa a saman ƙirjinsa, tabbas ba ƙaramin tsorata yayi ba, domin ba kaɗan ba aljanun nata sun girgiza shi, shi dai bai taɓa ganin tashin aljanu ba amma a ransa yana jin tsoron su tunda yana yawan jin labaran su, a baya lokacin da take ciwo yana ganin yanda Momy take fama da ita, a lokacin bai taɓa jin tausayinta ba kuma bai taɓa zuwa wurin da take ba, sai dai ya ja jiki ya koma ɗaki don ba ya son ma ya gansa kusa da ita, Sai ga shi yau sun tashi a gabansa, sai yanzu yake dana-sanin ƙin kiran Momy, ai da ta taimaka masa, Amma kuma ya ji daɗi da suka sauka da wuri, sai kallonta yake yi yana son ya je gare ta but babu hali, ga abincin sa da yake marari yana kallonta babu kaya breasts ɗin ta sun yi cirko-cirko suna tsole mishi ido, but babu halin mayar da kwaɗayi, sai faman haɗiyar yawu yake yi yana ci gaba da ƙare mata kallo amma ya kasa isa inda take, Sun jima a haka kamar yabar ta a haka yayi ta kallo ya samu Tv, Amma kuma haka nan ya daure ya nufe ta tare da ɗaukar ta ya manna ta a jikinsa, ɗakin ta yakaita ya ajiye ta a saman gadonta, Ya jima yana faman kallonta tamkar ya ɗaura hannu a abubuwan da suka tsole mishi ido, but yana tsoron ta farka, Blanket ya janyo ya rufe mata jiki sannan ya juya a sanyaye ya fice Tana jin ya rufo ƙofan; ta fashe da mahaukaciyar dariya har da tiƙo wa ƙasa tana shaƙe wa, yau ba ƙaramin muguwar dariya SHAREEF ya bata ba, a yanda ya rikice ya tsorata hakan ba ƙaramin nishadi ya sanya ta, dariya ta dinga yi har da riƙe ciki, "Oh! Yau nayi maganin wannan Bawa naka, ina ma da mai taya Ni ganin wannan draman? Hohoho Ni Maryamu." Sai ta sake kecewa da dariya tana miƙe wa tsaye, Bakin ƙofan ta koma ta saka key sannan ta dawo ta dinga tiƙa rawa tana dariya; farin ciki ya gama cika ta, "Wlh kaɗan ma ka gani, na gode Allah da ya nuna min tsoron ka a fili, ai kuwa na dinga maka haka kenan; sai na rama duk abubuwan da kayi min." Sai ta kama kumatun ta da dukka hannayenta, "nan gaba har da mari zan kwaɗa maka kaji inda daɗi." Faɗa wa kan gadon tayi ta kwanta tana rufe kanta, Cike da nishaɗi Maryamu a wannan lokacin tayi barci, barcin farin cikin da ya kwashe ta bata shirya mishi ba, har da murmushi a kan fuskarta. [26/04, 1:24 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE25* _____SHAREEF kai tsaye ɗakin sa ya koma, gaba ɗaya a sukurkuce yake don har yanzu jin sa yake yi cikin buƙata, ya ga samu ya ga rashi, dole ya shiga yayi wanka ya kimtsa kansa cikin riga da wando na shadda, mai ruwan omo, ba ƙaramin fitar masa da kyawun sa suka yi ba, kayan sun zauna mishi sosai sun ƙara bayyana hasken sa, sak Angon sa ya fito duk da babu hula a kansa, kuma fuskarsa babu walwala sosai a dame take, Falo ya fita, yana fita ya hangi kayan Maryamu a yashe, zuwa yayi wurin ya ɗauka yana shinshina wa yana jin wani irin yanayi a tattare dashi, har wani lumshe idanu yake yi, Ya jima a haka before ya zuba kayan a saman kujeran yana nufan wurin Dinnig ganin akwai kaya a saman, Zama yayi shima ya haɗa tea ɗin ya shanye, sannan ya kora da gasashshen Kazan da ta rage, Bayan ya gama ya koma kujera ya zauna idanuwansa a kan ƙofan ɗakin Maryamu, ya jima a zaune yana ta faman tunani abubuwan da suka faru duk suka dinga dawo masa, ji yake yi tamkar ya buɗe ido ya sake tozali da ita a gabansa, ba ƙaramin nishaɗi abun da ya faru ya saka shi ba, har zuciyarsa yana jin wani sanyi yana ratsa shi sai dai baza ka taɓa fahimtar hakan a face ɗin sa ba. Lallai yanzu ya tabbatar da cewan ƊAN HAKIN DA KA RAINA... ga shi duk abin da yake buƙata a jikin Mace Maryamu tana dashi, idan da tun farko yayi haƙuri ya yi wa iyayensa biyayya da tuni an wuce wurin nan, ba wannan zancen ake yi ba, amma idanunsa sun rufe da soyayyar Haseena, bak'ar fatan Maryamu da kuma kasancewar ta ƴar ƙauye su kaɗai yake iya gani a baya, ashe bai san cewa tana da kyakkyawar surar jiki mai ni'ima da kyan kallo ba, ji be a ɗan ƙanƙanin lokaci yanda ta haɓake ta zama cikakkiyar Macen da ko yar shekaru 30yrs baza ta nuna mata komai ba, uwa uba yanda ta ɗauki wanka a yau face ɗin ta ya tsaya mishi a rai, dama shi mutum ne mai son kwalliya, abun da yake ƙara ƙauna kenan a wurin Haseena, idan ta caɓa ado ba ƙaramin tafiya da imanin sa take yi ba, yau sai ga shi ya ga inda makeup ya fi ɗaukar hankali, a fuskar Maryamu, a yau yake sake tabbatarwa tabbas kyakkyawar Mace kyakkyawa ce kawai, koda baƙa ce ko fara, tunda ga shi ya ga inda makeup yayi mugun yin ma bak'ar Mace kyau, skin ɗin ta very smooth and fresh, Mai ɗaukar hankali da kyan kallo, lallai babu abun da gyara bai saka wa, domin yana ji a ransa kawai don Maryamu ta samu inda ta huta ne har wannan kyawun ya bayyana a jikinta, ya san da tana ƙauyen can ne ai ko kashi sai ya fi ta kyau, ashe rashin gyara ne yake ɓoye kyawawa? Hmm numfashi ya ja mai ƙarfi yana miƙe wa tsaye, ya gaji da zaman shiru yana faman tunani; shiyasa ya nufi ɗaki ya ɗauki mukullin mota ya fita gidan, Bai da inda zai je dalilin da yasa ya wuce gidan su kenan Duk an watse ƴan biki, su Ammee kawai ya tarar a gidan ita da yaranta, itama a gobe zata wuce Abuja Bayan sun gaisa take tambayar shi Maryamu? Alhamdulillah kawai yace mata, Na'ilah na jikinsa ta maƙale mishi Dayake babu Momy a wurin sai ga ta ta fito daga ɗakin ta, ta sauko saman benen tana kallon shi Sai da ya bari ta zauna sannan ya gaishe ta yana wani sussunne kai ganin yanda ta kifa mishi manyan idanuwan nan nata Amsa shi tayi har lokacin bata janye ido a kansa ba, yayinda take mamakin yanda ta ganshi a wani sukuku kamar akwai abun da ke damun sa, domin Momy a cikin ƴaƴanta babu wanda ta fi karantar yanayin sa sama da SHAREEF, ko awanne yanayi yake tana saurin gane shi sai dai tayi shiru ta ƙyale sa, yanzu kuwa sai dai tace mishi, "ya Maryam ɗin? Ina fata tana nan lafiya babu wani abun da ya faru?" Kai a ƙasa ya amsa mata don ba ya son sake tozali da manyan idanunta sabida ya gane tuhumar sa take son tayi, shiyasa ya ƙi kallonta "Hmm Allah yasa dai da gasken ne tana lafiya, zan ma kira ta in ji dai." Dariya Ammee take yi, tace, "Oh! Aunty, na ga alamun kamar ba ki yarda dashi bane, ai tunda yace tana lafiya tana lafiyar ne." SHAREEF dai yana jin su bai ce komai ba, Har lokacin da su Aakifah suka fito suna gaishe shi, sannan ya ɗago kai ya amsa su yana bin su da kallo Suka zauna a kan kujera ɗaya, Aakifan take cewa, "Ammee don Allah zamu je mu sake ganin Maryam kafin mu wuce." Harara ta dalla musu, "ba na son yawon nan fa, baza ku je ba, tunda jiya kun je meye kuma zaku koma gidan?" Marairaice fuska suka yi, wannan karon Yusaira ce tayi magana tana cewa, "don Allah Momy ki sanya baki tabar mu, wlh baza mu daɗe ba." Momy tace, "ki bar su kawai su je, tunda ga Mijin nata ma ya baro ta ita kaɗai kar ta zauna cikin kaɗaici, ku kira Sadiq yakai ku tunda yana gida." Farin ciki ne ya cika su suka tashi suna ɓashe baki, da sauri suka wuce, Na'ilah ma ta bi su tana musu rigimar, "itama zata je." Yusaira ta aiki Na'ilan wurin Sadiq ta faɗa masa abun da Momy tace, Su kuma suka tafi ɗaki suka hau shirya wa, tunda dama sun yi wankan su kawai sauya kaya suka yi suka shirya cikin riga da skirt na atamfa iri ɗaya, don ba a bambanta musu kaya tamkar ƴan biyu aka mayar da su, su kansu suna jin daɗin hakan domin mutane da dama suna musu kallon Twins ne, since suna kama sosai, kuma ba kowa ya san Yaya da Ƙanwa bane tunda ba sa faɗa komin nacin mutum da son jin ƙwaƙwaf, kansu a haɗe yake sosai baza ka taɓa bambance su ba bare ka ce yaya da Ƙanwa ne tunda babu bambancin jikin su, Koda Maryamu ta koma can; sai yazamana itama iri ɗaya da kayansu ake mata, komai su uku ake musu, hatta Abee in zai siya musu wani abun tare yake siya musu, su Ammee basu taɓa bambanta Maryamu da ƴaƴansu ba, tabbas ba ƙaramin daɗin zama ta samu a can ba, don ita kanta a yanzu tayi baƙin cikin rashin komawar ta tunda sun saba Bayan sun shirya suka bar gidan har Na'ilah, Sadiq ya ɗauke su a Mota Aka bar Momy da Ammee suna ta zuba hiran su SHAREEF kuma na zaune a falon ya ƙi tashi, hankalin sa yana a kan wayansa amma jefi-jefi yana kallon t.v, tunda tashan MBC 2 ne sun saka Film mai kyau, dalilin da yasa ya ƙi tashi kenan yana kallon, Sai da aka kira sallah sannan ya je yayi ya koma ɗakin su ya kwanta abun sa sai barci, Bai farka ba sai kiran sallan la'asar ya tayar dashi, alwala yayi ya tafi masallaci Shima Dady ya dawo gidan lokacin, a tare suka dawo daga Masallaci, sai da ya tsare sa da tambayoyi a kan Maryamun yana tambayar sa, "Allah yasa bai muzguna mata ba?" Kansa ya shafa before ya amsa mishi Sosai Dady ya sake jan kunnensa a kan Maryamun a kan, "ya riƙe ta da amana, kar ya ci zalunta, ya kyautata zamantakewar su, idan ya ci amanar riƙon da aka ba shi tamkar ya ci amanar su ne, bazai taɓa yafe mishi ba." Tabbas jikin SHAREEF ba ƙaramin sanyi yayi ba, sabida jin furucin Dadyn, ya san da gaske yake yi tunda ya furta hakan, Bai dai ce komai ba har yayi musu sallama yabar gidan, Kai tsaye gida ya koma ya tarar da su Aakifah har yanzu suna nan Sadiq ma yana tare dasu bai tafi ba, yace, "ƙafanshi ƙafar su bazai je ya dawo ba, gwara a yi hiran dashi." Lokacin da ya shigo gidan ya tarar dasu suna baje suna hira sai dararraku suke yi, Har Maryamun wacce tuni ta sauya kaya ta saka kalan atamfar su, don zuwan nasu ne suka tashe ta barcin da take yi, Sai tsokanarta suke yi a lokacin da suka zo suka tarar da ita babu kaya, tunda kofofin rufe wa kawai SHAREEF yayi bai saka key ba, sai da suka shiga cikin falon suka ji shiru sannan suka wuce ɗakin Maryamu, Bayan sun kwanƙwasa ta farka, tana jin su ne ta buɗe musu ƙofan ko kaya bata sanya ba; illa blanket ɗin da ta rufe jikinta ta zo dashi har ƙofan ta buɗe musu Dalilin da yasa suke ta tsokanarta kenan suna dariya, musamman da suka ga kayanta a falo, Sai da suka gama shaƙiyancin su suka fada mata, "da Yaya Sadiq suka zo yana falo." Sai tayi maza ta ciro kayanta tana cewa, "irin naku ma zan sa, anko zamu yi wlh." Tana gama wa suka fita falon, A nan suka shantake suka yi ta hira har suka yi girki tare suka ci suka ƙoshi suka wanke komai, Sallah kaɗai ke tayar dasu Sadiq ma a falon yayi Sallah ya ƙi fita ya biye musu suna ta surutai Shigowar SHAREEF ne yasa suka dakata da hiran nasu, Yayinda idanunsa na a kan Maryamu yake amsa gaisuwar da suke mishi Ita kuwa ko ɗago kai ta kalle shi ta ƙi yi, sai yanzu ta soma jin kunyar abun da ya faru tsakanin su, takaicin da ya rufe ta kuma yanda ya gama ƙare mata kallo babu riga, Bata san sanda ta ɗaga kai ta watsa mishi wani kallo har da harara ba Waro ido SHAREEF yayi yana mamakin abun da tayi masa, Amma bai ce komai ba ya wuce ɗaki, Na'ilah na biye dashi kamar jela tana kiran sunan shi Aakifah ce ta raɗa wa Maryamu a kunne, "Mijinki fa ya dawo ki je ki tarbe shi, ba ki ga sai kallon ki yake yi ba." Dukan ta Maryamu tayi tace, "ban san iskanci fa." Daga Aakifan har Yusaira suka sheƙe da dariya, dayake suna wuri ɗaya har da tafa wa, Sai kuma suka haɗa kai suna ƙus-ƙus-ƙus Sadiq yace, "to gulman ya isa haka a tashi mu tafi, wlh ga kiran Ammee nan ma ya shigo, ku shirya mu wuce." Ya ƙare maganar yana daukar wayan Umarni ta ba shi a kan, "yanzu su dawo gida zaman ya isa haka nan." Dayake a handsfree ya saka wayan duk suna ji, Dolen su suka tashi suka koma ɗakin Maryamu suka hau kimtsa wa Bayan sun gama Yusaira tace, "Ma'am, ai sai ki je ki ɗauko mana Na'ilah a ɗakin sa tunda zamu wuce." Harara ta watsa musu tace, "Ai kuwa baku shirya tafiya ba kenan." "To kina nufin mu zamu shiga mu ɗauko ta?" A cewar Yusairan tana dalalo ido waje Sai ta zauna a kan kujera tana mayar da ɗankwali goshi da faɗin, "ahaf; ai sai kuyi kuma." Tsaki Sadiq ya ja yace, "kuna ɓata min lokaci don Allah." Aakifah tace, "to ai kana jin mu da ita, mun ce ta kira mana Na'ilah ta ƙi, kuma ka ga ba yanda za a yi mu je da kanmu." Wuce wa yayi zuwa ɗakin SHAREEF ɗin batare da ya ce musu komai ba, a bakin ƙofan ya tsaya yana nocking "Amma wlh kin ji kunya Maryam, ki sauya hali, Mace da Mijinta but sai shegen girman kan tsiya, bari ki ji Allah irin su Yaya SHAREEF ba abun wasa bane kin samu kar ki bari damar ki ta kufce, ki lallaɓa sa ki samu zuciyarsa tun kafin lokaci ya ƙure miki." A cewar Aakifah ƙasa-ƙasa take maganar kar Sadiq ya jiyo su Maryamu zata yi magana suka haɗa ido da SHAREEF da ya fito daga ɗakin tare da Na'ilah, ɗauke kanta tayi tana sake turo ɗankwali gaban goshi, ta miƙe tana cewa, "ku mu je in taka muku har bakin motan." Suma basu ce komai ba tunda suna ganin SHAREEF ɗin, Don tahowa yayi zai zauna a kan kujerar, Sai da suka yi masa sallama sannan suka bar falon Har bakin mota ta raka su, sai da ta ga sun shiga sannan ta mammaka musu duka tace, "tukuicin abun da ku ka yi min kenan, sai mun yi waya zan sake rama wa, don tsab nake da amsar maganar ku." Tana ɗaga musu hannu take ta dariya sabida ganin yanda suka sauya fuska sun ji dukan da tayi musu, "Ku gaishe min da su Ammee." Banza suka yi da ita har Sadiq ya ja motan zuwa bakin gate, Dayake ba a rigada an saka Mai gadi ba, dole shi ya fito ya bude ya fitar da motan, sannan ya zo ya rufe musu ƙofan Maryamu tana tsaye a wurin har lokacin; take mishi magana, "yaya Sadiq wai yaushe zaka koma ne?" Bai rigada ya fita ba sai yace mata, "zuwa jibi insha Allahu." "To Allah ya kaimu, don Allah ka sake zuwa kafin ka tafi." "No ba lokaci Maryam, na tafi." Ya ɗaga mata hannu ya rufe ƙofan Juya wa tayi ta shiga cikin gidan SHAREEF na zaune duk yana jin maganar da suka gama yi da Sadiq ɗin, dayake ƙofan falon a bude ne yana jiyo muryoyin su Tana shigowa suka haɗa idanu, sai da ta watsa mishi harara before ta ɗauke kanta ta nufi wurin kujeran, kayanta da ke wurin har yanzu ta kwashe ta nufi cikin ɗakin ta Yayinda SHAREEF yana kallonta but ya gaza yin mata magana, wani irin shakkarta ne ya kama sa, sai dai ido da ya zuba mata yana haɗiyar yawu kamar wani maye, lallai ɗan hakin da ka raina... A yau ga shi wacce ya raina ta ƙere wa sa'ar sa, Yana son ya bi ta yayi mata magana, amma kallon da take watsa mishi shi ne dalilin da yasa ya ji shakka ya kasa buɗe bakin sa, yana kallo ta shige ɗaki yana ji tamkar ya miƙe ya bi ta, Amma haka nan ya zauna a wurin yana jiran ko zata fito, sai kallon wurin yake yi Yayinda Maryamu kuma tana shiga ɗaki wayanta ta soma ƙara, wurin gadonta ta nufa tunda a kai ta ajiye, ta zauna a kan gadon tana duba wayan, Ganin sunan Innar su sai tayi saurin ɗauka tana kwaɗa mata kira cikin farin ciki "Hmm sallaman kenan kiran suna na wato? Ke dai baza ki taɓa sauya wa ba ko?" Tura baki tayi da cewan, "kai Inna, koyaushe baza mu riƙa maganar arziki ba sai kin min faɗa?" "Au iyee! Ni kike fada wa haka Maryamu?" "Sorry Inna, wlh suɓul da baka ne." Ƙwafa Inna tayi tana cewa, "za ki ci ubanki ne tunda ba ki da kunya, dama mai zai sa in kira ki in ba da dalili ba?" Kamar zata yi kuka tace, "ki yi haƙuri don Allah, wlh na sauya ba kamar yadda kika sanni bane a baya, nayi hankali." "Ni ba wannan yasa na kira ki ba, jiya da muka koma gida da dare Matar Yayanku Naziru ta haihu, na kira wayan Hajiya Khadijah ba ya shiga, idan kin same ta ki sanar mata." Farin ciki ne ya cika Maryamu, cikin murna tace, "wayyo Inna, ashe ina nan zuwa nan kusa?" "Kina nan zuwa nan kusan ƙaniyar ki, ke fa ba ki da hankali wlh, ki sanar mata da saƙon saura ki ce kin manta, na faɗa ne kawai don su sani ba wai zuwa zasu yi ba; bare ke ƴar kaɗan kaɗa miya, sha-sha-sha, kuma wlh idan ba ki natsu kin yi abun da yakai ki ba ke da mai sama, don aure ba abun wasa bane." Turɓune fuska tayi tace, "Inna meye kuma na min baki? Haba don Allah." "Ba baki nayi miki ba Maryamu, na san ba ki da hankali tunda har kika iya furta min maganganun nan a kan ba kya son auren nan, na san za ki iya yin komai, aure dai ibadan Allah ne, duk abun da kika yi walau mai kyau ko mara kyau akwai lada da zunubin da ake rubuta miki, shiyasa nace miki ke da Allan ki tunda yana kallon ki, gidan aure ba gidan wasa bane hanyar neman aljannar ki ne, duk abun da za ki yi kina tunanin babu komai to ana nan ana rubuta miki sakamakon shi, kuma za ki girbe abun da kika shuka, ki natsu Maryamu ki yi biyayya ga Mijinki, abun da yake so ki yi masa in har bai saɓa hanya ba, ban da rashin kunya wlh ki kiyaye kanki na faɗa miki, ke kaɗai kika samu wannan gatan duk a wannan gidan namu, kowa sai maganar ki yake yi, idan kika ce za ki yi wasa da damar ki za ki yi dana-sani a nan gaba Maryamu, mutanen nan sun ɗauki ragamar komai a kanki sun mayar da ke tamkar ƴarsu, duk abun da Yaya Ahmad zai yi wa ɗansa na cikin sa yayi miki domin gata, ki saka musu wurin yin biyayya ga ɗansu, kar in ji kar in gani Maryamu, na ja miki kunne kar in ji kar in gani. Ki gaishe da mai gidan, Umman Shatima ma tana gaishe ki." Daga haka ta kashe wayarta Tabar Maryamu da waya a hannu tana kallo kamar zata fashe da kuka, ba ƙaramin sanyi jikinta yayi ba, hakan ne yasa ta kwanta tayi shiru tana faman tunani, Daga baya sai ta miƙe zaune ta kira Momy domin sanar mata da haihuwar Sun jima suna waya da ita, har da Ammee duk sun gaisa suna ta mata nasiha suna ƙara wayar mata da kai a kan zamantakewar aure Bayan sun gama wayan ne ta miƙe ta fita, A lokacin babu SHAREEF a falon, kai tsaye kitchen ta nufa ta soma ƙoƙarin ɗaura girkin dare, duk da a lokacin kusan shida saura ne, kuma abincin da suka yi ɗazu babu yawa duk sun cinye, Dalilin da yasa take son girka wa kenan, maganganun Inna ne yasa ta ɗaura sanwan abincin su biyu Bare dama Momy ta sake jan kunnenta a kan girkin, "kar ta sake ta riƙa ɗaura abinci babu Mijinta, komai ta girka tayi da nasa." Tana aikin tana mita a yanzu, "ai wlh koda na ɗaura abincin nan ajiye wa zan dinga yi, idan bazai ci ba yabar sa in har Ni zan ce mishi ya ci, wlh sai na rama abin da yayi min don bazan yarda ba, dole ya san daraja na, Ni fa haushin sa nake ji, Ni fa na tsane shi wlh." "Kin tsane Ni ko?" SHAREEF yayi furucin da ke tsaye a bakin ƙofa tun soma maganar nata. [28/04, 8:50 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE26* _____Da sauri ta juya tana kallon shi, ko kusa bata san da zuwan shi wurin ba sai tsinkayan muryansa tayi, tsuke fuska tayi ganin yanda shima ya haɗe ran yana kallonta, Sai ta juyar da kai ta ci gaba da abun da take yi Tahowa yayi inda take, ya tsaya dai-dai bayanta kamar zai haɗe da ita Hucin numfashinsa ne ya sake ankarar da ita, ta juya da sauri tana bin sa da kallo, ganin shi gab da ita sai tayi saurin ja da baya tana haɗe wa da kantan kitchen ɗin, duk da haka babu tazara a tsakanin su, yatsina fuska tayi tana faɗin, "wai meye haka; ka zo ka tsaya min a nan kamar zaka faɗo jikina?" "So nake yi na faɗo ai, faɗa min waye kika tsana?" Ido cikin ido take kallonsa, batare da tsoro ko shakkarsa ba tace, "kai na tsana." Ta sake ƙwalalo masa ido, "na tsane ka nace, mugu azzalumi..." Saurin rufe mata bakin yayi da hannunsa ɗaya, "kar ki sake kira na da azzalumi." Ƙoƙarin cizon hannun take yi, sai yayi saurin cire hannunsa tun kafin ta kama mishi fata A fusace tace, "idan kuma na ƙi fa?" Tsira mata ido yayi, in cool voice yace, "zan yi haƙuri." Sai ta fashe da dariya, domin maganar nasa ba ƙaramin dariya ya bata ba, musamman da ta tuna abun da ya faru ɗazu; yadda ta ga tsoro ƙarara a cikin idanunsa While SHAREEF tsira mata ido yayi yana kallon yanda take ɓaɓɓaka dariyan babu ko ƙauƙauta wa, ba ƙaramin burge sa tayi ba, musamman da ya ga halittun dimples ɗin ta sun fito sosai zak irin nasa, sun yi mata mugun kyau, bai san lokacin da yakai hannunsa saman kumatun ta yana saka yatsansa ɗaya a ciki ba Hakan ne yasa ta dakatar da dariyan nata, yayinda suka zuba wa juna ido babu wanda ke ƙyafta wa a cikin su, still hannunsa na a cikin dimples ɗin ta har yanzu, Kamar shuɗewar wasu seconni suna a wannan yanayin, Yayinda Maryamu ta ƙyafta idanunta before ta saka nata hannun ta janye nashi, Idanunta a cikin nasa a yanzu ta yarfar da hannun tana mai sake haɗe fuska, "Kabar nan wurin, kar ka zo ka takura min ina aiki." Fuskarsa ya matso da ita sosai kusa da nata, a hankali ya furta, "zan taya ki ne, sabida in wanke kaina daga zargin da kike min a kan Ni mugu ne; azzalumi, ba na son kalman." "Ba ka so ko?" "Eh." "Ai kuwa kai mugu ne azzalumi, bazan taɓa manta abubuwan da kayi min ba, babu yanda zan yi ne nake zaune da kai cikin inuwa ɗaya a wannan gidan, baka tausaya min ba sabida ba ka so na, amma meye laifina? Don na nuna maka soyayya?" Sai ga hawaye sharr suna zuban mata, shiru tayi tana zare mishi idanu da cije laɓɓa sabida yanda take jin mugun haushin sa Ba ƙaramin mamaki take ba shi ba, yanzu sam ba ta shakkar gaya masa magana, sosai ransa ya sosu da furucin ta, amma ko a fuska bai nuna ba, sabida ba ƙaramin karaya yayi ba da ya hangi hawayen ta, tabbas a yanzu yana mata uzuri sosai domin yana ganin duk shi ya ja, Ganin ta juya zata ci gaba da aikin nata, sai ya sake matso wa sosai kusa da ita yana shinshina ta A fusace ta juya tana ture shi, "kai wanne irin maye ne? Kana takura min fa nace, meye haɗin ka da Ni?" "Sabida Ni Mijinki ne, ina buƙatar sauke haƙƙina da ke kanki." Wani kallo ta watsa mishi kamar idanun zasu faɗo ƙasa, cikin takaici tace, "wanne haƙƙin naka? Oh! Kana tunanin akwai wani abun da zaka samu a wuri na ne? Don ka ga na zama Mutum wato? To idan ka manta zan tuna maka, Ni ce dai sakaryan yarinyar nan ƴar ƙauye Bagidajiya, jahila ko? Ni ce Maryamu mai bak'ar fuska da ka tsana kake wulaƙanta ta, Ni ce dai ban canza ba..." Hannu yasa ya rufe mata bakin ta, sai ta buge masa hannun ranta a mugun ɓace take bin sa da mugun kallo, Before tayi magana ya rigata da faɗin, "kin canza mana, kin mugun canza wa, a yanzu ke abar so ne da sha'awar kallo, bazan iya zura idanu ina kallonki a haka ina cutuwa ba, abun da nayi miki a baya just ki manta, mu haɗa kanmu kin ji? Ina matuƙar buƙatar zama da ke, Please ki sauya daga yanda na sanki a baya mai nuna min soyayya ba irin wannan ba." Baƙin cikin maganar nasa ne ya cika ta, cikin ɗacin rai a fusace tace, "Ka san wani abu kuwa? Kuskuren da zaka yi shine kayi kokarin takura wa rayuwata a gidan nan, baka san me zan iya aikata maka ba, har yanzu baka san wace ce Ni ba, a baya kallona kake yi kawai sabida a lokacin soyayyarka ta rufe min ido, ta sauya Ni fiye da tunani, amma a zahiri ban canza ba, kawai dai ban nuna maka halina bane, wlh ban da mutunci, zan iya maka duk abun da na ga dama in har baka fita daga rayuwata kabar Ni ba, abun da kake nema baza ka samu ba." Lokaci guda ta ga ya fashe da dariya, abun da tunda take bata taɓa ganin sa yana yi ba, in fact ma ko murmushin sa ne bata taɓa ganin yayi ba, Saurin ɗauke kanta tayi a kansa sabida ba ta son ta ci gaba da kallon fuskarsa musamman yanda yayi mata kwarjini; tsantsan kyawun sa ya sake bayyana da fararen haƙoransa suke waje, Bata son ta nuna mishi lagon ta ya gane cewan maganarta kawai burga ce Hannu yasa ya juyo da kanta, idanunsa ya zuba mata cikin nata fuskarsa da murmushi yace, "Today I understand who you are, I know I was wrong in the past, but now I'm asking for your forgiveness for the things I did to you, bazan iya ganin laifin ki a komai da za ki yi min yanzu ba, zan lallaɓa ki sabida ina bukatar ki a rayuwata." Sai ya haɗe fuskarsu wuri ɗaya yana goga hancinsu, Tuni ta rufe idanunta; shi kuwa yana kallon nata face ɗin ne, "Thank you for all the things you have done for me in my life. I couldn't understand you before, but now I understand you more. Kar kuma ki ce I need something from you, Maryam, please be patient and forgive me." Eyes ɗin ta ta buɗe tana kallonsa cike da mamakin maganganun sa, bata taɓa tunanin da sauri haka SHAREEF zai iya sauya mata ba, bata taɓa tunanin zai iya ɗaukar ta wata aba a ƙanƙanin lokaci ba, Idanunta a kansa har ya juya yabar kitchen batare da ya sake ce mata komai ba, yayinda ta bi bayansa da kallo har ya fice, Anya shi ne? Tana kokwanto, ji tayi hawaye suna son cika mata ido, sai tayi saurin rufe face ɗin ta da tafukan hannunta, "amma ya cutar dani, taya ya zan iya yafe masa cikin sauƙi haka? Har yanzu ina jin haushin sa kuma ina jin soyayyarsa a wannan lokacin, ko dama soyayya da ƙiyayya suna haɗe wa wuri ɗaya?" Buɗe idanuwanta tayi, sai ta kama aikin da take yi amma ranta babu daɗi kuma wani gefen tana jin farin ciki, tana ji kamar zata iya manta abubuwan da yayi mata ta dawo da soyayyarsa, wai yau SHAREEF ne yake bata haƙuri, addu'o'in da ta dinga yi don ya fita a rayuwarta sai ga shi Allah ya sauƙaƙa mata komai, maganar sa gaskiya ne da yace So ba ya sauya wa, bakin da ya furta so; ko ya dawo ya bayyana ƙi ba gaskiya bane, soyayyarsa ita ce lagwonta kuma ƙaddaranta, baza ta taɓa sauya wa a zuciyarta ba, ko dai zata iya ba shi wani damar ne? Girgiza kanta tayi, a ranta tana tunanin har yanzu bai ce yana sonta ba, amma zahiri ya sauya mata, yanzu babu tsanar nan nata a idanuwansa, itama dole zata sassauta mishi ta ga iya gudun ruwan shi ko wani buri daga cikin zuciyarta zai cika Har sai da aka kira sallan magriba bata gama abun da take yi ba, sai da aka shiga Masallaci sannan ta gama komai takai saman dainng, after ta gama sai ta ɗibi nata abincin ta shige dashi ɗaki ta datse ƙofan ta Koda SHAREEF ya dawo sallah, jin shiru babu kowa a falo, yana ganin abincin a saman dainng ya san ta gama, don haka kai tsaye ɗakin ta ya nufa, but yana taɓa ƙofan ya ji a rufe, sake murɗa wa yayi ya ji gam alamun an rufe ta ciki, Kiran sunan ta ya soma yi a hankali yana cewa, "ta buɗe mishi kofan." Amma Maryamu tana jin sa sarai ta ƙi buɗe wa, tana zaune a saman gadonta tana cin abincin ta da hannu hankali kwance, har ya gaji da buga wa yana faman kiran sunan ta but tayi banza dashi Gajiya yayi yabar wurin ransa duk a jagule, haka nan ya koma ɗaki amma ya kasa haƙura, ya hau duba keys ko zai samu a dakin nasa, amma babu komai sai na dakin da ke bakin kofa, haushi kamar ya kashe sa, sosai ya ƙwallafa rai a kanta, a ganinsa maganar da suka yi ɗazu zata sassauta mishi ne, yana bukatar ta matuƙa, yana bukatar kasancewar su tare, Gajiya yayi da binciken ya kwanta da ɓacin ran, don ko wanka ya kasa yi bare ya je ya ci abinci duk da yunwar da yake ji, Yana kwance abun duniya ya ishe shi, da ya rufe ido Maryamu yake gani ya kasa barci sai juye-juye yake yi, Ganin yunwa ta addabe shi a yanzu, haka nan ya lallaɓa ya je saman dainng ya zauna, abincin ya buɗe, wanda har lokacin yana tururi tunda a coolern da ta sanya yana riƙe zafi, frd rice ne a ciki, sai yankakken hanta a ciki, Spoon kawai ya ɗauka ya saka a ciki ya hau ci, daɗin abincin yasa ya ɗan ci da yawa sannan ya rufe ya nufi fridge ya sha ruwa, after ya gama ya koma ɗaki ya sake kwanciya, haka ya dinga juye-juye yana tunanin ko dai ya sake zuwa ya bata haƙuri ne? Duk da bai da tabbacin zata bude mishi ƙofan, tabbas bazai iya zama da ita na tsawon lokaci a haka ba, dole ne yayi wani abun amma bazai hakura da ita ba, wata zuciyar tana faɗa masa, "mai zai hana ya nemo maganin barci yayi mata amfani dashi?" Amma tuna abun da ya faru ranan nan da bata yi barci ba, sai duk ransa ya sake ɓaci, Yana a wannan yanayin kuma sai ga kiran Haseena, abun ya ba shi mamaki domin rabon shi da ita ya manta, bazai iya tunanin tsawon lokacin da ta ɗauka bata amsa call ɗin sa ba har ya gaji da kira, A yanzun ma ya ƙi ɗauka har tayi mishi two missed call, ƙarshe sai ya kashe wayan ma, don a yanzu ba kaɗan ba mugun haushin ta yake ji, ta cutar dashi a rayuwa, ta juya mishi baya a lokacin da yake bukatar ta, ko ya amsa wayan ma babu amfanin da zata yi mishi, har yanzu yana baƙin cikin yanda ta ƙi tausaya wa rayuwar shi, duk da irin ƙaunar da suke yi wa juna, a yanzu kuwa ya soma samun sauƙin raɗaɗin da yake ji a kanta, don haka ba ya bukatar kiran ta a dai-dai wannan lokacin, Haka yayi barci cikin wani hali cike da mafarkin Maryamu, Koda ya tashi da asuba sosai cikin sa yake ciwo, ƙarshe a ɗakin yayi Sallah, ya duba maganin sa babu saura, Haka ya kwanta yana murkususu har garin Allah ya waye, daƙyar ya tashi yayi wanka ya sauya kayan sa ya fice a gidan zuwa asibiti Wurin ƙarfe tara da rabi sai ga kiran Hanif ya shigo wayansa, lokacin ya fito daga wurin likita, jikin da ɗan sauƙi tunda har sai da ya kwanta ya samu relief a office din, Sai da ya shiga mota sannan ya amsa kiran Hanif ya fara sallama, ya amsa mishi, Sai yace, "ko dai har yanzu kana barcin ne na tashe ka?" "No, yanzu haka ma ina asibiti fitowana kenan." "Asibiti kuma? Me ya faru ne?" Ya tamabaya hankalin sa a ɗan tashe, don yayi tunanin wani abu ne But sai SHAREEF yace mishi, "na je wurin Doctor Abbas ne, magunguna ne suka ƙare na je ya duba Ni." "Haba! Wai kana nan a haka har yanzu baka yi abun da ya dace ba? Me kake jira to?" "Mai nake jira kake tambaya?" "Eh, sabida nayi tunanin an wuce wurin nan Bro, musamman a halin da kake ciki." Ɗan numfashi ya ja before yace, "Hanif ba yanda kake tunani bane, na kasa samun damar yin komai, ka san abubuwan da suka faru a baya a kan abun da nayi mata, so ta ƙi bani wannan damar." Dariya ya sheƙe dashi, "wai to kai biye mata zaka yi? Haba sai ka ce ƙaramin ƴaro Bro da har zaka bari Maryam tayi maka wayon? Ai ina ga akwai hanyoyi da dama da zaka iya bi da ita, har yanzu Maryam yarinya ce, cikin sauƙi zaka iya sarrafa ta, musamman ma da ta kasance akwai soyayyarka a tare da ita, ba abu ne mai wuya Maryam ta tsane ka ba wlh, kome kayi mata zaka iya sauya ta a cikin ƙanƙanin lokaci, sabida tana sonka, baza ta taɓa ƙin ka ba, soyayyarka ita ce raunin ta, Bro be a man mana, kar ka zauna zaman jira kwaɗo yayi maka ƙafa." Shiru SHAREEF yayi yana sauraron sa, sai kuma can yace, "yanzu dai kabar wannan maganar ka bani shawara, amma ba yanda kayi zato bane, haƙiƙa a yanzu na soma sanin wace ce ita, kuma har cikin zuciyata ina son kasancewa da ita, ina jin farin ciki da ganin ta cikin gidana, ina jin wani abu a game da ita sosai, sai dai ba kamar Haseena ba, don ba na tunanin soyayya ne." "Hmm wai kana nufin har yanzu ba ka kaunar Maryam? Har yanzu Haseenan kenan ita ce a cikin ranka?" "Ban ce maka ba, ina nufin soyayyar da nayi a baya, ba kalan ta nake yi wa Maryam ba, abun da nake ji a game da ita, ba irin wacce na saba ji bane a baya a cikin soyayyata." Hanif yace, "sabida ita nata soyayyar daban ce, amma baza ka gane hakan ba sai lokacin da ka rasa ta a rayuwa, kana son Maryam Bro, a yanzu soyayyarta na tare da kai, shawara kawai ka bi duk yanda za ka bi domin ku daidaita kanku, babu amfanin ci gaba da zama a haka, ka faɗa mata gaskiyar kana sonta ku zauna ku fahimci juna, ita soyayya tana son fahimtar juna ne, idan masoya suna fuskantar matsala, yana da kyau su zauna su fahimci juna, idan suka tattauna zasu gano matsalar su, tattaunawa tana da matuƙar muhimmanci a rayuwar masoya, duk abun da ke cikin zuciyarka ka faɗa mata, babu bukatar ɓoye wa, itama a wanann lokacin zata fahimce ka; kuma zata bayyana maka sirrin da ke ranta, duk abun da take ji a ranta zata zayyane maka, daga nan kuma sai kuyi maganin matsalar ku, don Allah Bro ka daure kayi hakan, kar ka tsaya tunanin babu wata soyayyarta a ranka, kawai ka furta mata ko meye." Ajiyar zuciya SHAREEF ya sauke, cike da sanyin murya yace, "shikenan zan yi hakan, zan yi abun da ka ce min." Sai ya ɗan ja tsaiko before ya sake furta, "Thank you." Dariya Hanif yayi, sai yace, "muna nan zuwa, zan kawo Amaryata su gaisa da Maryam, amma bazan jima ba don zan wuce mu haɗu da wani Likita da muka soma magana a kan matsalar My Amrah, so zan kaita ne kawai in ajiye ta." "Ok, but bazan koma ba gaskiya, zan je Company don ina buƙatar in je in hadu da Mahmud mun yi waya da shi." Daga nan suka yi sallama, Har ya ajiye wayan sai kuma kiran Haseena ta shigo wayansa, Tsayawa yayi yana kallon Phone din, Sai da ta katse kiran ta sake kira before ya ɗaga, amma ya ƙi yin magana yayi shiru yana sauraron ta Daga can muryan Haseena ya bayyana, ta kira sunan sa da faɗin, "dear, Wai me ke faruwa nake kiran ka kake ƙin ɗauka? I called you yesterday night but baka yi peaking ba, after all ka san da cewan muryanka nake buƙatar ji, tunda ka ji na kira ka ka san da hakan." Wani irin ɓacin rai ne ya ziyarce shi, lallai yarinyar nan ta raina mishi hankali, muryansa a kausashe wanda ya kasa ɓoye ɓacin ransa yake cewa, "oh! Haka ne? You need to hear my voice, that's why you call me ok? I thought you forgot me in this world  ban zaci hakan ba, Haseena, nayi mamakin abubuwan da kika aikata min, ina bin ki kamar ƙaramin Yaro, na ƙasƙantar da kaina duk sabida ina sonki, ina azabtuwa da kaunarki, ina buƙatar ki a cikin rayuwata, amma ba ki gane haka ba, lokaci guda kika juya min baya, kika kasa bani farin cikin da nake bukata, Haseena stop pretending that you love me after now I have no use for you." Mamakin furucin sa ne ya cika ta, domin ta san cewa SHAREEF bai taɓa gaya mata irin waɗannan maganganun ba tun sanda ta samu damar ƙara cusa mishi soyayyarta a zuciya, a kullum in ya kira ta roƙon ta yake yi da magiya yana kuka da idanunsa, amma a yau kuma abun mamakin har ya samu bakin gaya mata magana, don haka tace, "Dear, Ni kake fada wa haka? Ko ka manta wace ce Ni?" "Ban manta ba Haseena, ke ce Haseena wacce ta kasa faranta min a lokacin da nake buƙatarki, You chose my sadness over my happiness ko? To ai ban ga amfanin ci gaba da zama da ke a haka ba, karatu ne dai ki je ki ci gaba da yi, bazan hana ki ba, but ba da igiyar aure na ba, babu amfanin ci gaba da rayuwa da wacce a yanzu ba ta so na, I know Haseena you have changed me, I will give you this chance, because now I myself stop feeling your love in my heart, ina ga gwara mu rabu kowa ya je yayi rayuwarsa yacce yake so, abun da ba ki sani ba, a baya na ɓoye miki cewan ina da aure, before na aure ki iyayena sun yi min Aure, amma na watsa musu ƙasa a ido; na zaɓe ki fiye da farin cikin su, na kasa musu biyayya duk a sabida ina sonki, sai dai a yanzu babu amfanin ci gaba da nuna miki wannan soyayyar, zan zaɓi in zauna da zaɓin su sabida a yanzu itama zaɓina ne, a yanzu haka ta tare a ɗakin da kika ƙi ki tare. I have no more worries now Haseena, na sake ki..." Daga haka ya gimtse wayan batare da ya jira jin mai zata ce mishi ba, don a yanzu mugun haushin ta da yake ji ko kusa bazai iya bata damar da zata ci gaba da masa magana ba, kuma ba ya sonta cikin rayuwarsa, gwara ya rabu da ita kawai ya huta tunda haka ta zaɓa, tabbas soyayyarta bata masa rana ba, Haseena ta cuce shi ta ci amanarsa, wanda bai taɓa tunanin hakan ba, sabida irin yardan da ya bata, duk wanda ya ci amanarsa ba ya iya yafe masa cikin sauƙi, a yanzu bata da sauran amfani a rayuwarsa, Motansa ya ja da gudu yabar haraban asibitin, yayinda yana jin kiran wayan nata, hakan ya ƙara fusata shi, nan take ya tsayar da motan ya kashe wayan gaba ɗaya sannan ya ci gaba da tuƙin sa. Juma'at Mubarakh fans. [29/04, 7:44 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE27* _____Dayake Hanif ya kira Maryamu ya sanar mata da zuwan nasu, Lokacin ta farka kenan tana kwance tana duba wayanta sai ga kiran sa, ta ji daɗin jin cewan zasu zo, shiyasa da sauri ta miƙe ta soma aikace-aikace, Gyara ɗakin ta ta soma yi sannan ta gyara falo, ko kusa bata bi hanyar ɗakin SHAREEF ba, bata damu da yana nan ko ba ya nan ba, aikinta kawai take yi, Daga ita sai rigan barcin ta doguwar riga mai santsi kalan ruwan ƙasa, kanta kuma ta kwafa hula mai tambarin UB a gaban, red colour yana da tuntu, Tsab ta gyara gidan ta saka turaren ƙamshi, sannan ta kwashe komai na saman dainng ta nufi dashi kitchen, sai da ta buɗe abincin ta ga alamun SHAREEF ya ci, Bakinta ta taɓe ta zubar da sauran ta soma wanke-wanke, bayan ta gama sannan ta ɗaura girki, Cikin sauri take yin komai kar su zo bata gama ba, Jallop ɗin taliya ta ɗaura, shiyasa cikin sauƙi ya soma dafuwa, sai tayi using da sauran naman da aka ajiye mata, dama raguwa ne tun na washe garin ranan da aka kawo ta, Sadiq ya siyo ma su Ammee da suka zo gidan suka zauna, tare da kayan ciki, jiya ta ƙarisa amfani da hantan da ya rage, yau kuma ta zuba sauran raguwar Kazan, babu wasu kayan cefane a gidan duk da an tsibira kayan abinci kala-kala, shima kayan tea ɗin da suke amfani dashi duk su Ammee suka sanya Sadiq ya kawo su, dayake ba yawa a yanzu ma ya gama ƙare wa Tana ganin ya soma sulale wa ta wuce ɗaki ta shiga wanka, Bayan ta fito ta nufi kitchen ɗin daga ita sai towel ta ƙarisa sauran aikin, sai da ta zuba a cooler sannan ta koma ɗaki tana ƙoƙarin shirya wa, Riga da skirt na material lace ta ɗauka ta sanya, mai ruwan ƙwai da ratsin dige-ɗigen milk, tana cikin shafa lotion ta ji shigowar motan su, bata tabbatar da su bane shiyasa ta ɗauki ɗankwalinta ta ɗaura, ko powder bata saka ba ta fice a haka after ta zura flat shoes, Tana fita kuwa sai ta ji nocking, hakan ne ya tabbatar mata da su ne, tunda in SHAREEF ne ya san ƙofan a buɗe take bazai tsaya nocking ba, Wurin ta nufa ta buɗe musu tana washe baki Hanif da Amra ne tsaye dukkan su sun sanya kaya iri ɗaya shadda kalan purple, light purple, Yayinda Amra tayi using da dogon hijab har ƙasa shima purple ɗin dack, ta sanya flat shoes da Jakar hannunta kuma farare, Ba ƙaramin kyau tayi ba, dukkan su sai shining suke yi ƙyallin aure ya bayyana a fuskokin su, Bata yi kwalliya ba amma ta saka jan Jambaki da yayi mata kyau sosai Hanif yace, "Ƙanwata kin ganmu sai yanzu." Dariya tayi tace, "ku shigo mana." Ta matsa musu a hanya suka shiga Tare suka nufi cikin falon, While Hanif da Amra suka zauna a kan two sitter, Ba ƙaramin kyau suka yi ba domin sun dace da juna Maryamu kuma sai da ta nufi fridge ta ɗauko musu ruwa da lemo, sannan ta zo ta zauna Hanif yace, "Bro bai dawo bane har yanzu?" Dayake bata san ya fita ba, sai kawai tace, "eh bai dawo ba." "Ok, mun yi waya dashi ai, ya ce min ya fita, To ga Amaryata na kawo miki, fatan za a kula min da ita don Ni ba zama zan yi ba?" "Kai Yaya Hanif, tun yanzu zaka tafi? Ka bari mana ga abinci sai in ɗibo maka ka ci, kuma ai Yaya SHAREEF ɗin ba ya nan tunda ka ce kun yi waya ka bari ya dawo." "Aa dawowarsa ba yanzu ba, nima zan je in ga Likita ne a kan matsalar My Amrah, goben nan zata soma ganin Likita insha Allahu, muna bukatar addu'ar ki Allah yasa a dace." Duban Amran tayi, tana murmusawa tace, "insha Allahu Yaya zan taya ku da addu'a, amma wlh tana da kyau Yaya, ka iya zaɓe, ta fi ka kyau fa, har dogon hanci ta fi ka." A yadda tayi maganar ba ƙaramin dariya ta basu ba, Daga shi har Amran suka dara Itama tana dariyan tace, "wlh da gaske nake yi Yaya." Ya dube ta yace, "wai haka My Amrah?" Dariya tayi tana rufe fuskarta cike da kunya "Kinga kin sa ta jin kunya, amma duk da haka fa kin faɗi gaskiya." Murmushi Maryamun tayi, tana tsiyaya musu ruwan a cup ta basu, tare da cewan, "wlh ba wasa ba Yaya ta burge Ni sosai, ina sonta da ƙawa. Duk da dai kamar ta girme Ni, amma zan riƙa kiranta da Aunty." Dariya Hanif yayi yace, "ban da abun ki, ai ko ta girme ki ke ce Matar Yaya, ita ce zata ce miki Aunty, ki ɗauke ta kawai tamkar ƙawar taki, don zan so ku haɗa kanku sosai, ita kanta tana da sister wacce na san zaku zo kai ɗaya da ita, sunanta Afra, jiya ta zo gidanmu ta wunin mana, kinga da yau ne ta zo da mun zo tare kin ganta." "A'a, Ni dai na fi son Aunty Amra, ita ce ƙawata. Ko Aunty amra? Za ki amshe Ni a matsayin friend ko?" Kanta ta gyaɗa mata da sauri tana murmusawa, domin hakan yayi mata dad'i, musamman yadda ta ga Maryamu ta saki jikinta da ita, bata nuna mata ƙyama ba, sabida Hanif ya bata labarin ta yace, "ita yar uwansu ce, auren zumunci aka yi da SHAREEF." So a ganin ta baza ta amshe ta hannu bibbiyu ba, ko a yanayin da ta ganta akwai iyayi; sai kuma ta ga Maryamun ba haka ba, ta saki jikinta sosai da ita Hanif bai jima ba yace, "zai wuce." Ruwa kawai ya sha yayi musu sallama ya tafi, sai da ya sumbaci Amran sannan ya fice Yana fita Maryamu tace, "gaskiya Yaya Hanif yana sonki, kun yi matuƙar burge Ni, wlh in faɗa miki gaskiya, Yaya Hanif yana da kirki sosai, ke kam kin dace, nayi farin cikin wannan auren naku ba kaɗan ba, Allah ya ba ki lafiya kema ki riƙa magana kamar kowa." Murmushi Amra tayi cike da jin daɗin zantukan Maryamun, sai dai bata da bakin magana illa kallonta da take yi fuskarta a washe ta kasa dena murmushin Yayinda Maryamu kuma dayake akwai shegen surutu ne, musamman da Amran take burge ta, sai tahau mata tambayoyi a kan yanda suka haɗu da Hanif din, Ganin tayi shiru ta ƙi bata amsa sai dariya take, Hakan yasa ta tuna bata magana, sai tace, "ki yi hakuri fa na manta da ba kya iya magana, kuma ga shi ban iya irin Yaren ku ba, ya zamu yi kenan? Don wlh ina son muyi hira sosai." Amra dai bata ce mata komai ba illa sauraron ta da take yi, Ita kuma ta samu bakin zuba sai rattafa zancen ita kaɗai take yi, shiyasa idan tayi abun dariya sai dai Amra ta dara kawai cike da nishaɗi A tare ma suka ci abincin, kamar sun jima da sanin juna, don sosai Maryamu ta ja ta a jiki kamar tun farko ta jima da sanin ta, yanda ta saki jiki da ita ita kanta tana mamakin hakan, bata san cewa Maryamu bata da nuna rashin sabo ba, musamman in ka shiga ranta, Dole Amra ta biye mata wurin biye mata tana mayar mata da martanin maganar nata ta hanyar waya, Ita kuma sai Maryamu ta amsa ta karanta, Hakan ne yasa hiran nasu tayi daɗi sosai suna ta bada labarin junan su, Ta hakan ne har Maryamu ta san labarin haɗuwar su a wurin aiki Yayinda Maryamu itama ta saki baki ta dinga rattafa mata labarin soyayyarta da SHAREEF, ta faɗa mata yadda ta so shi so ba kaɗan ba, "duk da a wannan lokacin tana jin haushin shi da kuma tsanar sa, amma maganganun da ya fada mata a jiya yasa ta ji sauƙin komai, jiya ta kwana cikin tunanin sa tamkar soyayyarsa ta dawo sabo a tare da ita, tana jin tabbas baza ta iya rabuwa da SHAREEF a rayuwarta ba, domin shi ƙaddaranta ne, sai dai kuma abubuwan da yayi mata ya cutar da ita ba kaɗan ba, ta kasa manta komai har yanzu tana kallon abun da yayi mata a idanunta," sai tayi dariya a karshen maganar nata, ta sake duban Amran tace, "na so in tsane sa ya babu wani tamkar sa, sai dai ashe abun ba mai sauki bane a gare Ni, soyayyarsa ita ce ƙaddarata, a kansa na gane raunina, ada ina kallon kaina tamkar babu wanda yakai Ni Jarumta, kin san me? Hawayena suna wuyan fita a cikin idanuna, ina da taurin rai matuƙa, amma kuma; tun sanda na soma jin labarin sa, mafarin soyayyata a gare sa kenan, batare da na soma tozali da shi ba, tun a lokacin na san cewa Ni maƙurar mai rauni ne, domin na kasa ɓoye soyayyarsa koda na ɗan ƙanƙanin lokaci ne, a lokacin ne hawayena suka samu damar zuba, na zama mahaukaciya a kansa, ina jin a lokacin bazan iya rayuwa babu shi ba, idan har ban same shi ba mutuwa zan yi, na azabtu gaskiya kuma bai tausaya min ba, ina ji a raina a lokacin tabbas ba yin kaina bane, sabida ciwon da ya same Ni a wannan lokacin, na so na koya wa kaina tsanar sa, amma ashe hakan ba zai faru ba. Kin san maiyasa nake baki wannan labarin nawa?" Ta ƙare maganar fuskarta a washe cike da farin ciki Yayinda Amra kuma ta cika da tausayinta, tana kallonta ne tamkar ta zubar mata da hawaye, idanunta sun cika da ƙwalla, sai ta girgiza mata kai alamun a'a Ita kuma sai tace, "sabida ina son ki bani shawara ne, a raina na ji cewar na zayyane miki komai, sabida a dai-dai wannan lokacin ke ce a tare da Ni, duk abubuwan da yayi min, kina ganin ya dace in yafe mishi da gasken yana son zama dani in manta da komai? Ra'ayin ki kawai nake bukata domin ba na son in ci gaba da bin ra'ayin zuciyata." Shiru Amra tayi tana kallonta, sai kuma tahau mata rubutu tare da bata shawarwari a game da jin ta bakin ta, tabbas ta nuna ta tausaya mata, amma ta nuna mata cewan, "haƙuri shi ne ya fi komai a gare ta, bata da wani zaɓi face hakan, domin duk wanda yayi haƙuri a rayuwarsa wata rana zai yi dariya." Ta sake nuna mata matukar dacewan su da SHAREEF, kuma ta nuna mata, "tayi Sa'a sosai, babu amfanin ci gaba da ƙuntata mishi matuƙar ya nuna nadamar sa a gare ta, don haka kawai tabar komai ya wuce ko don samun farin ciki a tare da ita." Sosai Maryamu ta ji daɗin shwaranta, kuma ta yarda har zuciyarta tabbas ta yafe wa SHAREEF komai, komai ya wuce, baza ta sake tuna abubuwan da yayi mata ba, Don haka suka ci gaba da hiran su gunun sha'awa Haƙiƙa Amra ta ji daɗin haɗuwa da Maryamu, ita kanta bata taɓa bama wani dama a rayuwarta kamar yadda ta ba Maryamu ba, ta saki jikinta sosai da sosai da ita A haka suka jima har magriba sannan Hanif ya dawo ɗaukar Amra, Kuma har wannan lokacin SHAREEF bai dawo ba, Yana can gidan su yayi zaman sa can tun sanda ya dawo daga Company, yana can yana tunanin yanda zai yi ya shawo kan mutumiyar tasa Yayinda itama take zaune a gida tana faman jiran sa, Inda a dai-dai wannan lokacin har wanka tayi ta cakare ta zauna a falo tana faman jiran sa, tana riƙe da wayan ta ta hau kan facebook tana karanta labarai sai dariya take yi tana nishaɗi A wannan lokacin aka dauke wutan NEPA, ko'ina yayi duhu sabida kusan ƙarfe takwas da rabi saura ne a lokacin, Wayan hannunta tayi saurin kunna wa tana haska falon, ta ajiye a saman kujera ta ci gaba da kwanciyar ta, tana lissafin yadda zata tarbi SHAREEF ta ba shi mamaki, Dariya ta kwashe dashi, sai kuma ta ji dariyan nata yana fita bibbiyu tamkar ana kwaikwayon ta, hakan ne yasa ta dakatar da dariyan tana miƙe zaune idanunta a zare a waje cike da mamaki, abun ya matuƙar bata mamaki, amma don ta tabbatar da abun da ta ji maybe kunnenta ne, sai ta sake kece wa da wani dariyan, yayinda ta sake jin dariyan yana fita da karfi kuma bibbiyu, gidan yana amsa wa da ƙara, Da sauri ta gimtse bakin ta tana ƙara zare idanu, a wannan lokacin mamaki ne kawai ya cika Maryamu amma babu ko ɗigon tsoro a tare da ita, don ita mace ce da ba komai ne yake saurin tsorata ta ba, koma wa tayi ta kwanta tana cewa, "oh! Illan sabon gida kenan, sai kayi haƙuri." Sai ta ja tsaki tana ɗaukar wayan nata ta ci gaba da latsa wayan, Wanda yake ɗebe mata kewa na ɗan wani lokaci Can kuma sai ta soma jin iska yana kaɗa wa sosai har yana ɗaga Curtin ɗin Falon, tashi tayi ta nufi wurin windown ta soma rufe wa, Har ta rufe sauran, ya rage saura guda ɗaya, tana ƙoƙarin rufe wa sai ganin ƙatuwar bak'ar Mage tayi a saman windown, ko kafin tayi wani ƙwaƙƙwaran motsi Magen nan tayi wani uban sufa ta ɗare mata jiki, Ƙara ta saka tana wurgi da wayan, ta soma kiciniyar cire Magen a jikinta, amma inaa; ta maƙalƙale ta tana kai mata yakushi mai mugun azaba, wanda tuni ta rikirkitar da Maryamun nan da nan ta fita a hayyacinta ta faɗi ƙasa tana ihu da kururuwa, tsoro da tashin hankali gami da tsananin ruɗin ganin wannan mummunar Magen yayi matuƙar razanar da ita, kuka take yi sosai tana son fincike Magen a jikinta amma inaa ta kasa, kokawa suke yi sosai duk da yadda take yakushin ta tana cizon ta tana son cire ta a jikinta amma ta kasa, ga azaban da ke ratsa ta duk inda ta kafa mata ƙumba, kuka sosai Maryamu take yi duk ta fita a hayyacinta ta haɗa zufa kashirɓan ga hawaye shaɓe-shaɓe, Daƙyar ta samu nasaran fincike ta a jikinta duk ta gama yaga mata riga ta ji mata ciwuka a wuya, tana yin nasaran wurgi da ita tayi wani irin ƙundunbala tana shirin gudu wa, daƙyar ta iya tashi ko ganin gabanta ba ta yi; ta ranta a guje zata shige dakin ta, sai dai rasa ƙofan da tayi yasa ta buga kanta da bango, wani uban ihu ta fasa idanunta sun rufe tuni ta afka cikin ɗakin ko ganin gabanta ba ta yi, Da lalube ta ƙarisa bakin gadonta jikinta na rawa kamar mazari ta haye ta ƙudundune tana kuka da salati Gurnani ta soma ji cikin ɗakin alamun Magen ta biyo ta, Ai kuwa nan ta hange ta sabida tana iya hango idanuwanta masu ban tsoro da jan haske kamar walƙiya Da sauri ta toshe bakinta hawaye na ziraran mata tsoro da firgici gami da tashin hankali sun cika ta, Tana ganin ta yo sufa zata faɗo kan gadon, A guje ta miƙe bakin ta na ambaton salatin da bata san mai take furta wa ba, domin a lokacin Maryamu ta sadakar ta mutu bata taɓa ganin irin wannan bala'in ba, Tana sauka saman gadon ta harɗe ta faɗi a wurin, Magen ta kawo mata cafka tayi saurin riƙe mata wuya, Yanda suka soma kokawa tana ƙoƙarin yakushe ta amma Maryamu ta riƙe mata wuyan gam ta shaƙe ta kamar zata kashe ta, tsoron da take ciki bata san ma mai take aikata wa ba burin ta kawai ta ceci kanta daga mummunar Magen, Sai kawai ta samu ta dinga buga kanta da ƙasa babu ƙaƙƙauta wa, Magen na kuka kamar kukan Kura amma Maryamu ta ƙi ƙyale ta tunda ta samu wannan damar, kamar mahaukaciya haka ta koma tana dukan Magen ko ta ina, Hakan bai yi mata ba sai da ta wawura inda zata samu abun bugu, nan hannunta ya taɓo Kujeran dressing mirror, da sauri ta miƙa hannu ta taɓo wurin mirror inda kayan kwalliyar ta yake, kwalban turare ta cafko ta samu ta buga mata Magen ta tsandara wani uban ihu mai kama dana Mutum, Lokaci guda Magen ta ɓace ɓat a hannunta Hakan ba ƙaramin razanar da Maryamu yayi ba, ta sake ɗimauce wa lokaci ɗaya ta rarrafa ta miƙe ta bi hanyar ƙofa, tana zuwa dai-dai bakin ƙofan ta sake buga kanta da bango a kokarinta na neman ƙofan fita, nan ta saka ƙara ta faɗi a sume babu numfashi a jikinta Wanda a dai-dai wannan lokacin SHAREEF ya dawo gidan, yayi siyayyan kaya maƙil a ledoji, ya kwaso kayan ya fito zuwa cikin gidan, sabida akwai duhu shiyasa yayi amfani da touch light na wayansa ya shigo cikin Falon, A nan ya hangi hasken wayan Maryamu a yashe wurin window, tsaya wa yayi yana kallon wurin, sai kuma ya nufi cikin falon ya ajiye siyayyan da yayi mata, wayan ya ɗauko cike da mamakin ganin ta a wurin a yashe, Tunaninsa ya ba shi ko dai tsoro ta ji har tayar da wayan nata tunda babu wuta a gidan, don haka ya nufi ɗakin ta kansa tsaye ya burma, ya kusa cin karo da ita a ƙasan sai ya hange ta yashe kanta ya fashe yana zubar da jini, A kiɗime ya duƙa gabanta yana kallonta cikin tashin hankali da al'ajabin halin da ya tsince ta Ga ta nan a yashe goshin ta ya fashe, yayinda riganta kuma gaban rigan ya yage gaba ɗaya sai bra ɗin ta, wuyanta duk yakushi da kuma alamun cizo da yake tsittar da jini Da sauri ya sanya hannu ya tallabo ta yana kiran sunan ta cikin tsananin tashin hankali da tsananin ruɗe wa, ya rasa ma abun yi sai faman kiran sunanta yake yi yana girgiza ta, Sai kuma yayi saurin ajiye ta ya ƙarisa yage rigan jikinta tunda mai taushi ne kamar vest, saurin ɗaure mata kanta yayi ya miƙe a guje ya fita Falo, ruwa ya dauko ya dawo domin yanda hankalinsa ya tashi a tunaninsa ta mutu ne, fargaba yasa ya diddila mata ruwa yana kiran sunanta da ƙarfi jikinsa na rawa kamar mazari, ya kasa ɗaukar ta bare ya fitar da ita zuwa asibiti, kawai burin sa ya ga ta farfaɗo tana da rai, jikinsa sai kerma yake yi haka ya koma ya sake ɗauko wani ruwan ya diddila mata A take a nan ta kawo numfashi mai ƙarfi, sai dai a firgice ta tashi tana ihu da ƙoƙarin miƙe wa ta gudu Riƙe ta gam yayi ya matse ta a jikinsa yana faɗin, "ki natsu, ki natsu, Ni ne.. Ni ne." Haka ya dinga maimaita wa yana sake matse ta kamar zai mayar da ita cikinsa, har hankalin sa ya soma kwanciya sabida tabbatarwan da yayi tana da sauran rai, amma ba ƙaramin ruɗe wa yayi ba, sosai ya ƙanƙame ta yana rarrashinta, sai da ya ga ta soma dawowa cikin hayyacinta Sannan ya ɗago ta yana tambayarta abun da ya same ta? Kuka Maryamu ta fashe dashi tana haki jikinta sai rawa yake yi, har yanzu tsoro da fargaba bai bar ta ba, daƙyar ta iya furta masa, "don Allah ka taimaka min ka cece ni, zata kashe Ni." Mayar da ita jikinsa yayi ya sake ƙanƙame ta, hannunsa ɗaya a saman kanta suna zaune dirshan sosai a wurin, hura mata iska ya soma yi sabida yanda ya ji jikinta na fitar da gumi, yayinda yake furta, "ki natsu mana, babu abun da zai faru da ke, muna tare, oya faɗa min wace ce zata kashe ki? Faɗa min kinji kar ki ji tsoro I'm here with you." Duk da tsoron bai bar ta ba, don gani take yi kamar Magen zata dawo mata, har gizau take mata a cikin idanuwanta, shiyasa ta sake ƙanƙame shi ko numfashin kirki ba ta iya yi sabida yanda ta haɗe fuskarta da jikinsa, daƙyar ta iya faɗa masa abun da ke faruwa, don sai da ya dinga rarrashinta sannan Shi kansa yayi mamakin abun da ta faɗa masa, amma mai zai kawo Mage cikin gidan su? Fahimtar da yayi ta tsorata sosai ko iya ɗago ta ba ya yi a jikinsa, gaba ɗaya ta manne mishi, shi kansa daƙyar yake numfashin bare ita, ta ƙi bari su tashi a wurin suna zaune yana ci gaba da rarrashinta, duk ya shiga damuwa a sabida ganin halin da take ciki, don kuka ta dinga mishi dole ya ci gaba da rarrashin nata daƙyar ya samu tayi shiru, Shi da kansa ya ɗauke ta suka koma saman gado, yayi ƙoƙarin ajiye ta but ta ƙi bari kuka ta fasa mishi tana cewa, "don Allah ka tafi dani, wlh bazan iya zama ba, tsoro nake ji." "Is ok, babu abun da zai faru da ke, maybe ta shigo ne but bari in je in duba sai in fitar da ita." Ƙanƙame shi tayi ta hana shi zuwa, duk yanda ya so ya fita ya je ya duba amma Maryamu ta hana sa, kuka sosai take yi a wannan lokacin, domin ba ƙaramin tsorata tayi ba, ga azaban inda Magen ta ji mata ciwo Sai yace mata, "bari yakaita asibiti a duba ta, bazai yiwu ta kwana a haka ba." Amma Maryamu ta ƙi, sam ta ƙi yarda, shi kansa ta hana sa ya jirga, dole ya ɗauke ta suka fita a tare ya rufe musu ƙofa tunda baza su kwana a haka ba, sannan ya dawo da ita ɗakin ya ɗaura ta a kan gadon, ya so yin wanka nan ma ta ƙi barin sa, yanda ta manne mishi bai da yanda zai yi haka nan ya biye mata suka ƙudundune a kan gadon, Dama SHAREEF yana bukatar hakan, yau ga dama ta samu, a zuciyarsa sai ya ji dadin wannan yanayin, nan kuwa ya fara amfani da damar sa wurin sauya salon kwanciyar nasu, daga rarrashi abun ya sauya, sabida bazai iya jurewa suna a manne da juna a wannan yanayin ba, duk da halin da take ciki amma hakan bai sa ya kasa fito da maitan sa a fili ba, A hankali ya soma shafa ta tun yana yi cikin lallami sai kuma abun ya soma zarce wa Maryamu tana jin sa bata da yanda zata yi don ba ta son ta motsa daga jikinsa ko kaɗan, a lokacin da ya soma laluban bakinta sai kawai ta buɗe masa bakin nata sabida ita kanta ta soma fita a hayyacinta sakamakon haɗuwar su wuri ɗaya, take ta mara masa baya ta ba shi haɗin kai; nan da nan suka haukace wa juna. [01/05, 8:49 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE28* _____Hawaye ne ke zuba a cikin idanunta, cikin ƙunan rai da fitan hayyaci take cewa, "ya ci amanata, bazan taɓa yafe mishi ba, ya cuce Ni, nayi masa iyaka da kowacce Mace amma ashe ban yi nasara ba, ashe yana da wata Matar ya muna-furce Ni?" Cike da ɓacin rai Nana ta katse ta da faɗin, "ki yi shiru haka nan, kinga halin da kike ciki, why did you make this decision and not inform me? You know how much I love you, if anything happens to you I will never let her go, dole sai na ɗauki mataki, Haseena na faɗa miki ki fita harkan wannan Yaron, yanzu kin gane ba kya gaban shi ko? Babu amfanin ci gaba da rayuwa dashi." Sai ta tallabo ta cike da lallami tace, "zan iya miki komai baby, ki manta dashi tunda kin ga ya ci amanar ki, I will not tolerate whatever happens to you, zan ɗauki mataki." Zaune Haseena ta tashi tana kama goshin ta cike da raɗaɗi, hawaye na ɗiga a face ɗin ta tana kallon Nanan tace, "bazan iya jure ganin SHAREEF da wata ba, Ni kaɗai ce wacce yakamata ya so, dole sai na raba su bazan haƙura ba, in har Ni na cika Haseena wlh sai na ɗanɗana musu ƙuɗan su, tunda har ya rabu dani sai dai kowa ya rasa." Sai tayi shiru tana jan numfashi zuciyarta na matukar tafarfasa, yayinda take duban Nanan ta sake cewa, "a yanzu dole ne in nuna wa SHAREEF na fi ƙarfin yayi min wannan cin amanar, bazan taɓa yafe masa ba." Kamo hannunta Nana tayi tace, "What do you want to do? I will help you ko mene ne; because I don't want to see you in this situation, tell me now?" "Ina son in raba tsakanin su, in har bazai dawo gare Ni ba na gummaci in sadaukar wa da ƙungiya shi, amma bazan taɓa bari wannan yarinyar ta ɗauke min shi daga gare Ni ba, sai na ɗanɗana mata azaba sai na kashe ta itama." Wani irin farin ciki ne ya mamaye zuciyar Nana, cikin jin daɗi take faɗin, "Weldon Babyna, abun da yakamata ki yi kenan, babu amfanin ci gaba da soyayya dashi, kawai ki sadaukar da shi ki samu salama daga ranki, i know kin san da cewan wannan lokacin za a buƙaci jini a wurin ki, za ki zabi ɗaya ko iyayenki ko kuma wanda kika fi ƙauna a zuciyarki." "Sai dai in sadaukar dashi, amma ba na son abun da zai raba Ni da iyayena, shi kuma babu amfanin ci gaba da rayuwa dashi bayan yayi min alƙawarin duk runtsi bazai rabu dani ba, amma ga shi lokaci guda ya ci amanata." Ta ƙare maganar cikin baƙin ciki Yayinda Nana take rarrashinta cikin kwantar da murya, tana faɗa mata, "ta kwantar da hankalin ta komai zai wuce, nan ba da jima wa ba zasu yi maganinsu". 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____Har kusan ƙarfe shida na safe babu wanda ya farka a cikin su, domin wani irin barci suke yi mai cike da kwanciyar hankali, musamman ma SHAREEF wanda ya fi samun natsuwa barcin sa yake yi cikin farin ciki sakamakon abun da ya wakana a tsakanin su, Shi ya fara farka wa a wannan lokacin, yayinda ya bi fuskar Maryamu da kallo, wacce take ƙudundune a jikinsa tana sharan barci sai numfarfashi take yi, duk da barcin nata yayi nisa amma koda gani akwai ɗan rashin natsuwa a tattare da ita, Musamman da ya ji jikinta da ɗan zafi, sai ya daura hannunsa a saman goshin ta ya ƙura mata ido yana ƙare mata kallo, ba ƙaramin farin ciki ne a kan fuskarsa ba, wani irin nishaɗi ne yake tattare dashi sabida samun abun da yake so, Duk da har a zuciyarsa bai so hakan ta kasance a lokacin da take cikin wannan halin ba, ya so ya tausaya mata amma ya gaza, ya gaza riƙe kansa balle ya haƙura, dole ne yasa ya aiwatar da hakan, amma shi kansa ya jinjina mata kuma ta ba shi tausayi matuƙa, A hankali ya zare jikinsa ya sauka daga kan gadon, Sai dai ya kasa tafiya sai da ya jima yana kallonta ganin yanda take ta numfarfashi tana jujjuya kwanciyar ta, Sai da ya ga kuma kamar ta koma barcin ta dena motsi before ya fita a dakin ya koma nasa ɗakin, Wanka yayi ya nemi riga da wando masu taushi ya saka a jikinsa, Sannan ya gabatar da sallan asuba da basu samu sun yi ba, Dawowa dakin yayi, ya tarar da Maryamu har yanzu tana barcin bata farka ba, Zuwa yayi bakin gadon ya tsira mata ido yana faman murmushi, sai yanzu hankalin sa ya kwanta ya samu abun da ya jima yana bukata, yau yarinyar da ya raina ta ba shi farin cikin da bai taɓa samun sa ba a tsawon rayuwarsa, yanzu ya kara gasgata cewan akwai bambanci tsakanin su da Haseena, domin a yanda ya samu Maryamu a cikakkiyar budurwan ta hakan ya fi komai faranta mishi, hakan na nufin shi ya soma sanin ta, nashi ce ita, shi kaɗai, Zama yayi a gefen gadon while yana bin gashin ta da kallo ganin yanda ya cure wuri ɗaya a cinkushe, hannu ya sanya zai taɓa gashin, sai kuma ya ɗaura a kan goshinta, amma kuma zafin da ya ji sosai hakan ne yasa ya cire hannunsa da sauri, nan da nan murmushin kan fuskarsa ya gushe ya sake mayar da hannun yana sake taɓa wuyanta zuwa kanta, alamun zafin zazzaɓi ne don yanda ya ji jikin zauu hakan ya tsorata shi, Bazai yiwu ya barta a haka bai kaita asibiti ba, ko don raunin da ke kanta da kuma ƙananun ciwukan da Magen ta karce ta, sai yanzu ne ma yake ganin yakushin da kyau daga saman wuyanta zuwa ƙirjinta, sosai ta karce wurin har ya ƙafe ya bushe da jini, don ma kwanciyar da suka yi duk sun kwashe, Ƙoƙarin tayar da ita yake yi wurin hura mata iska daga bakin sa A hankali ta soma motsa wa tana mimmiƙe ƙafafunta, kamar wucewar seconni ta soma motsa idanunta zata bude su, a hankali ta buɗe manyan idanuwanta da suka yi luhu-luhu suka canza launi, daƙyar ta iya buɗe su tana kallonsa, sai dai tuni tayi ƙoƙarin mayar da su sabida zafin da ya soma ratsa ta daga kanta, wani irin ciwon kai ne ke addabar ta ban da azaban da ke ratsa ta na saman goshin ta, hannu ta soma ƙoƙarin kaiwa wurin Amma sai yayi saurin riƙe wa yana cewa, "sorry, kar ki taɓa, forgive me please, na kasa control na kaina ban tausaya miki a halin da kike ciki ba, but sorry zan yi ƙoƙarin taimaka miki yanzu sai mu je asibiti, i know kina jin ciwo sosai ko?" Cikin lallami yake maganar a kuma sanyin muryan nan nasa Wanda hakan ne yasa Maryamu ta ƙoƙarta ta buɗe idanuwanta ta zuba mishi, sai dai babu wani walwala a kan face ɗin ta, kallon sa kawai take yi tana ɗan runtse idanunta Hakan ne yasa ya gane tana jin jiki, don haka ya dinga bata haƙuri kamar zai ari baki, shi da kansa yayi ƙoƙarin ɗago ta Bata yi musu ba duk yanda yayi da ita haka take bin shi, sai dai ta mayar da idanunta ta rufe saboda ciwon kan da ke addabar ta, ko kusa ba ta son ta motsa kan, sosai ta soma jin yana ƙaruwa sabida moving da yake yi da ita, sai cije laɓɓa take yi tana sakin huci da ƙara Nan da nan SHAREEF ya ruɗe ya rasa yanda zai yi, musamman yanda ya ga hawaye suna zuba a idanunta kuma ga shi ta kasa buɗe idanun, sai faman kiran kanta take yi ta manne masa tana kuka, Sosai ya tausaya mata; kuma bai gushe wajen bata hakuri ba har suka shiga toilet, shi da kansa ya haɗa ruwan ɗumi tunda an dawo da wutan tun asuba, Sai ya kunna shower ya soma mata wankan, a lokacin ba ƙaramin kai zuciya nesa yayi ba; domin wani irin mugun sha'awarta ne ya sake taso mishi musamman yanda ya ga surar jikinta a waje, sai dai ya kasa taɓuka komai sabida a halin da take ciki tana kuka daƙyar ta tsaya yayi mata wankan, Wankan tsarki yayi mata before ya saka sabulu sama-sama ya wanke ta, da sauri yake yin komai har ya gama ya fito da ita sai sannu yake mata, Doguwar riga ya ɗauko mata na atamfa, sai da ya tsaya ya dubo hijab dogo har ƙasa fari ƙal, sannan ya saka mata ya sure ta zuwa waje, Har sun kai wurin motan ya tuna bai dauko car key ba, dole ya koma da ita tana manne a jikinsa sai ƙanƙame shi take yi, jikinta har ya soma rawan sanyi sakamakon ruwan da ta shiga, hankalin sa ya ƙara tashi sosai haka ya dauki key ya zo ya saka ta a front seat, sannan ya zagaya ya shiga ciki ya ja zuwa bakin gate, fita yayi ya buɗe cikin sauri ya fitar da motan, sai ya dawo ya rufe ya ja ya tafi, Hannunta ya kamo yana kallonta fuskarsa da tsananin damuwa, a hankali ya furta, "is ok Baby, don Allah ki yi hakuri yanzu zamu je asibiti a duba ki." Shiru yayi kuma ya ci gaba da tuƙin, yayinda ya soma laluba aljihun sa don ya kira Doctor Abbas, but babu wayan ya barta a gida, haka nan ya haƙura ya ci gaba da tuƙin a cikin ƙanƙanin lokaci suka iso asibitin, Shi kansa ya soma tsorata da yanda ya ga Maryamu take yi a yanzu, sai mimmiƙa take yi tana kuka sosai, jikinta yayi zafi zauu kamar garwashi, Ɗaukan ta yayi da gudu ya nufi cikin asibitin da ita, babu wasu mutane sosai tunda safe ne, Amma duk inda ya gibta sai an kalle shi ganin sa rungume da ita yana tiƙan gudu, Kai tsaye office din doctor Abbas ya nufa Ya ci Sa'a yana nan tunda shi ne a kan duty, yana zaune yana duba wasu files sai jin bugun ƙofa yayi, ko kafin yayi motsi sai ganin SHAREEF yayi a ciki ya nufo inda yake, Hakan yasa shima ya mike da sauri yana tambayar sa lafiya? "Please Doctor, give her emergency help, I think it's a fever in her body, please do something." "Is ok, ɗaura ta a gadon mu gani." Doctorn yayi maganar yana nufan wurin gadon shima, Bayan ya daura ta sai ya soma duba ta, daga bisani ya ɗago kai yana kallon SHAREEF da ke tsaye a wurin hankalin sa a mugun tashe, don gani yake yi har da laifin sa maybe kusantan ta da yayi ne a halin rashin lafiya, "S. Ahmad ka kwantar da hankalin ka Please, ka samu wuri ka zauna, insha Allahu ba wata matsala alamun zazzaɓi ne mai zafi ya rufe ta, but yanzu zamu bata taimakon gaggawa." "No Doctor, ka duba ta ina gani, hankalina zai fi kwanciya." Murmushi doctor Abbas yayi, sai dai bai ce komai ba ya ci gaba da duba ta, amma ya tambayi SHAREEF ɗin abun da yasa ta ji ciwo haka? Bai ɓoye masa komai ba ya sanar masa, sannan ya kara da ba shi labarin neman ta da yayi yace, "ya nemo doctor Mace ta duba ta, maybe ya ji mata ciwo ne." Smile doctor yayi sabida jin abun da yace, sosai yake ganin kishi a tattare da SHAREEF ɗin ganin yanda ya kasa ya tsare a wurin, ya kasa ma bari a cire mata hijab sai dai ɗaga wa aka yi, Don haka a haka yayi mata treatment bayan ya gama duba ta ya gane matsalar ta Ba wani abu bane illa zazzafan zazzaɓi da ya rufe ta, dama akwai wasu mutane haka suke idan ciwo ya kama su nan da nan yake rikitar da su ya fitar da su a hayyacin su, wasu ma har sambatu suke yi kamar sun zauce, jikinsu bai da jimirin ɗaukan ciwo nan da nan yake rikitar da su, To itama haka jikin Maryamu yake, bare da tsoron da ya ƙara taimaka wa nan da nan zazzabin ya samu gurbin zama a jikinta, ga kuma ciwukan da ta samu, at the short time suka fitar da ita a hayyacinta Sai da ya gama yayi masa bayanin komai, sannan ya kira wata Likita Abokiyar aikinsa, ya faɗa mata matsalar da kuma binciken da zata yi a kanta, Dole aka ɗauki Maryamu a keke zuwa wani ɗakin, A can Likitan ta duba ta, so babu wata matsala ba wani ciwon da ya ji mata, amma duk da haka ta ɗan taimaka mata, Kuma ta yi wa SHAREEF bayanin, "kawai ruwan ɗumi za a taimaka mata tana shiga shikenan, amma ba wata matsala." Sai kuma wasu magunguna da ta rubuta wadda zata sha Shima Doctor Abbas ya rubuta mata na zazzaɓin, sannan ya ɗan basa wasu shawarwarin Har hankalin SHAREEF ya kwanta musamman da ya samu Maryamun jikin da ɗan sauƙi tana barci, dole ya jira don ta tashi, but bai sanar da kowa ba haka ya zauna shi kaɗai a asibitin yana jiran farkawar ta. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____Shima Hanif suna can ganin Likitan Amra, duk da a bayanan Likitan bayan ya duba ta, yayi musu bayanin, "zai yi wuya ta koma tana magana gaskiya tunda ciwon ya rigada yayi mata illa da yawa, sai dai zasu yi ƙoƙarin daura ta a kan magani zuwa nan da kamar sati ɗaya su gani." Domin ita kanta Amran tayi musu bayanin a baya an taɓa mata magani lokacin da cutar ya same ta, Babanta ya kashe kudi don samun lafiyarta, amma duk inda suka je sai a ce musu, "zai yi wuya ta warke." Har na gargajiya sun gwada duk ba a dace ba, amma dai a wancan lokacin an samu ci gaba tunda ada ba ta iya fitar da sautin dariya ko kuka, but da aka tashi mata da magani sosai shine sautin dariyan ta yake fita, har idan tayi dariya za a iya jin sauti, ko kuma idan tana kuka ana jin sauti kaɗan; ba kamar lokacin da ta soma ciwon ba, Wannan cigaban kawai aka samu Ga shi yanzun ma an basu rashin ƙwarin gwiwa, sai duk ta damu, hankalin ta ya kara tashi sosai Amma kasancewar akwai Hanif a tare da ita, haka ya dinga bata haƙuri yana kwantar mata da hankali, ya nuna mata, "zai yi iya ƙoƙarin sa wurin sama mata lafiya, ko'ina zai iya kaita in har za a dace, domin bai da sauran farin ciki a yanzu ban da ya wuce ta samu lafiya kamar kowa." Tabbas ta yarda cewa komai Hanif zai iya yi sabida farin cikin ta, yanda yake nuna mata kulawa da ƙauna tamkar ya babu wata kamar ta a duniya, matuƙa tana farin ciki a yanzu bata da wani sauran damuwa, in har zata kasance dashi to rashin lafiyarta ba komai bane a wurin ta, Don haka koda suka koma gida sai tayi masa bayanin, "kawai ya hakura da neman maganin ta, domin tana ji a jikinta baza ta taɓa warke wa ba, ita a yanzu tana farin ciki fiye da koyaushe, samun sa ya fi mata komai, kar ya ɓatar da kuɗin sa a banza babu biyan buƙata." Kallonta yayi, sai ya ajiye wayan da ya gama karanta reply ɗin ta, yayinda ya janyo ta jikinsa yana cewa, "babu maganar ɓatar da kuɗi a banza My Amrah, idan har don ki samu lafiya ne Ni zan iya kashe ko nawa ne domin ganin kina magana kamar kowa, zan fi jin dadin hakan, ai Ni nace zan yi ko? To ki dena faɗin haka, soyayya ya sanya nake miki komai, idan har ina tare da ke a duniyar nan, komai baza ki nema ki rasa ba, zan yi iya yi na domin faranta miki insha Allahu, mu jira kwanakin da Likitan ya ɗiba mana, idan ba a samu ci gaba ba zan yi ƙoƙarin nema mana wata ƙasa mu fita domin dace wa." Sai ya sanya hannunsa a saman kumatunta tare da ɗan matse mata gefe da gefen kumatun, yana murmushi yace, "kar ki sake faɗin haka kin ji ko? Kuɗina kuɗinki ne, ina matuƙar ƙaunar ki My Amrah, please smile domin samun kwanciyar hankalina." Murmushi tayi tana kallonsa, sai kuma ta rungume shi sosai a jikinta bakin ta na ɓari kamar zata yi magana amma ta kasa, nan da nan hawaye suka cika idanunta tana jin matukar soyayyarsa a rai, tana fatan Allah ya barta da ranta domin faranta wa wannan Bawa nasa, bata taɓa tunanin akwai ranan da zata samu mai ƙaunarta kamar Hanif ba, Sosai ta ƙanƙame shi; ta ƙi ba shi damar ya ɗago bare ya ga hawayen da take zubar wa, Duk maganar da yake yi amma ta ƙi yarda ta ɗago, sai ta lafe a jikinsa tayi shiru idanunta a rufe tana sauraron yanda yake shafa mata baya Domin ko bata faɗa ba ya gane a halin da take ciki, don haka shima yayi shirun yana faman shafa ta; tsawon lokaci suna a haka babu mai motsi. [02/05, 10:37 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE29* _____After Maryamu ta farka; jikin nata da ɗan sauƙi ba kamar yanda aka kawo ta ba, kawai kanta ne yake mata ciwo kaɗan-kaɗan sai kuma rashin ƙarfin jiki, Bayan ta yi wa Likitan bayani sai yace, "ba komai a hankali zata samu sauƙi, tana soma shan magani zata koma normal." Sai yace ma SHAREEF, "ya ɗauke ta kawai su tafi babu wani damuwa." Shi da kansa SHAREEF ya taimaka mata ta sauka a kan gadon, sannan ya riƙo ta gam bayan sun yi sallama da Likitan ya fice da ita, a haka ya nufi da ita haraban asibitin kamar zai mayar da ita ciki don yanda yake ta faman mata sannu Maryamu na jin sa amma ta kasa ɗago kai ta kalle sa, musamman in ta tuna abun da ya wakana a tsakanin su, amma wani irin daɗi take ji a yanda yake bata wannan kulawan, bata zaci hakan ba don ba karamin mamakin sa take yi ba, Shi da kansa ya buɗe mata gaban motan ta shiga, sannan ya rufe ya zaga ya shiga ya ja motan, Hannunsa ɗaya ya ɗaura a saman nata hannun ganin ta kwantar da kanta ta rufe ido, Hakan ne yasa ta buɗe manyan idanuwanta da har yanzu a tashe suke sun ɗan kaɗa sun yi narai-narai dasu, Tana kallonsa suka haɗa ido, sai tayi saurin janye nata idanun tana rufe wa da sauri Shi kuma face ɗin sa akwai damuwa sosai yake duban ta yana tuƙin, a hankali yake cewa, "I'm sorry, I don't hurt you but na kasa ba ki kula wa sai ma ƙara miki damuwa da nayi, please ki yafe min." Shiru Maryamu tayi, amma tana mai cike da mamakin sa sabida wannan furucin, yau ina zata saka kanta don farin ciki? wai dama wannan ranan tana nan zuwa da SHAREEF zai nuna mata kulawa kamar haka? Ko dai ya fara sonta ne? Idanunta a rufe ta ƙi ta buɗe su, but tana sauraron yanda yake matsa mata hannunta a hankali jefi-jefi yana mata sannu, Babu wanda ta amsa har suka isa gidan Ya tsayar da ita yace, "ta bari ya buɗe mata ƙofan." Ledan maganin ya ɗauka sannan ya fita zuwa side ɗin ta, da kansa ya buɗe mata ya kamo hannunta, sai da ya fitar da ita sannan ya jinginar da ita a jikinsa before ya rufe ƙofan, Ai kuwa kamar Mage haka ta lafe mishi still har yanzu bata buɗe ido ba, Ganin haka sai ya ɗauke ta cak zuwa cikin gidan Saurin bude ido tayi tana zuba mishi, ganin sun haɗa ido yasa tayi mishi murmushi tana sake manne mishi, A haka suka ƙarisa ciki ya sauke ta a saman doguwar kujera Sai da ya ajiye ta sannan ya ajiye maganin a saman Centre table, "Let me give you the medicine because the doctor said to give it to you when we go home, I'm coming." Wurin fridge ya nufa zai ɗauko ruwa, jin da sanyi sosai sai ya fasa ɗauka ya wuce kitchen ya tara cup a famfo ya ɗibo mata, Sannan ya dawo ya zauna a gefen ta bayan ya ajiye ruwan, Kallonta yake yi ganin ta rufe ido ta kwantar da kanta tana ɗan sakin numfashi, A hankali ya sanya hannu ya soma cire mata Hijabin jikinta before yace, "yanzu mai yake miki ciwo? Please tell me na ga har yanzu kamar kina jin jikin?" Murmushi tayi masa tana girgiza mishi kanta, sai kuma a hankali tace, "nothing." "Are you sure?" Kanta kawai ta ɗaga masa still da murmushi a kan face ɗin ta, don ba ƙaramin daɗin yanayin take ji ba, duk da ciwon da take fama dashi kaɗan-kaɗan Hannu ya sanya a dimples ɗin ta guda ɗaya, ya tsira mata ido kamar zai cinye ta tare da furta, "I have never seen someone who is as beautiful as you are, but now I see your beauty, and you are more beautiful than me." Dariya ta fashe dashi Ba ƙaramin daɗi ya ji ba; da ya ga haƙoranta a waje, sai tayi masa mugun kyau, shima murmushin yayi before yace, "Allah da gaske nake yi." Sai ya ɗan ja numfashi ya ƙara da furta, "Thank you, thank you for everything, today I'm happy kin sanya Ni farin ciki, farin cikin da ban taɓa jin irin sa ba, nayi miki gurguwar fahimta, wanda hakan yasa na cuci kaina da farko, sabida wasu ra'ayoyi nawa." Sai ya ɗago kanta ya kamo haɓarta suna kallon idon juna, yayinda yake furta, "i love You, i love so much! ki yafe min abun da nayi miki a baya, a yanzu zan ba ki kula wa sosai babu wani sauran tsanarki a cikin zuciyata, na yarda zan zauna da ke." Idanunta ne suka soma cikowa da hawaye, sai tayi saurin lumshe su tana jin wani irin farin ciki a ranta, Rungumetan da yayi ne yasa hawayen idanun nata suka zuba a saman kuncinta, da sauri ta sanya hannu itama ta ƙanƙame shi kamar zasu mayar da juna cikin jikinsu Yayinda tuni shi ya ɗaura bakinsa a saman wuyanta yana sakar mata kiss cikin ƙauna da marari, lokaci ɗaya ya soma bin ta yana sumbata wani irin tarin sha'awar ta na ƙara huda sa Daƙyar ta iya kwace jikinta sabida yanda yake shinshina ta yana sakar mata kissing ko ta ina, har ya soma ƙoƙarin saka hannunsa a cikin riganta, Sai ta janye jikinta tana mayar da numfashi kanta a ƙasa Shima haka zalika numfashin yake sauke wa yana riƙe da hannunta gam idanunsa a kanta, sai da ya ɗan ɗauki lokaci a haka before ya daidaita natsuwarsa, har idanunsa sun kaɗa a haka yake kallonta kamar zai cinye ta, don ba ƙaramin buƙatar ta yake yi ba a yanzu, amma bai da yanda zai yi dole ya ɓoye zalamansa a ciki tunda ko a yanzu jin jikinta yake yi ya ɗauki ɗumi ba kamar yanda suka shigo ba, Hannu ya sanya ya sake ɗago haɓarta suna kallon juna, "Sorry, bari in ba ki maganin ki." Kanta ta girgiza mishi, sai kuma ta bi sa da kallo da yake ƙoƙarin ɓallo mata maganin, Sai tace, "No bazan iya sha a haka ba, ka haɗa min ko tea ne sai in sha dashi, koda ruwan sanyi ne." "Ok hakan ya fi miki?" "Eh." "Ok, ina zuwa." Miƙe wa yayi ya je zai haɗo mata Tana biye dashi da ido duk inda ya gibta, wani irin daɗi da farin ciki na ratsa ta, yau dai ga shi ta samu SHAREEF a hannunta, abun kamar a mafarki, har sake ware ido take yi tana sake ƙare masa kallo a ranta tana jin kamar barci take yi, ta samu soyayyarsa, yau shi yake faɗa mata kalman so, daɗin da take ji yasa sai sakin murmushi take yi, mai ya fi wannan daɗi; a ce yau kana tare da wanda kake matuƙar ƙauna a rayuwarka? Tabbas zama da masoyi a inuwa ɗaya akwai dad'i, daɗin da ba ya misaltuwa, Sai da ta ji motsin sa zai dawo sannan ta duƙar da kanta Zama yayi a gefen ta sannan ya miƙa mata tea cup ɗin Amsa tayi sannan ta amsa maganin, da ɗaya-ɗaya ta haɗiye su har ta gama, Ta dube sa tana yatsina face before tace, "ina son yin wanka, zan yi sallah." "Ok mu je ɗaki sai in taimaka miki." Idanu ta zuba mishi, ganin da gasken yake yi har ya miƙe tsaye yana shirin ɗaga ta Sai ta marairaice fuska cike da shagwaɓa kamar zata yi kuka ta noƙe da faɗin, "um um, kai ne zaka yi min wankan?" Ba ƙaramin tafiya dashi tayi ba, don sai da ya ji wani yamm tsigar jikinsa ya miƙe cike da tsananin sha'awarta da ke gudana a cikin jinin jikinsa, koma wa yayi ya zauna tare da ɗago ta zuwa jikinsa, sai ya rungume ta tamkar ƙaramar yarinya, cikin lallami da sassanyan muryansa, dama in ta wurin murya ce akwai shi da kashe ta kamar wani Mace, Nan fa ya soma rarrashinta yana cewa, "haba babe, just wanka ne fa; ko ba ki ga halin da kike ciki bane? Yanzu ai mun wuce wannan wurin sabida a yanzu babu abin da zan riƙa barin ki kina yi, komai Ni zan miki, zan nuna miki ƙauna da kula wa fiye da tunanin ki, ina son in wanke kaina a wannan time ɗin, please Babe?" Ya kare maganar yana ɗaura bakin shi saman nata Ba ƙaramin kashe mata jiki yayi ba, musamman yanda numfashin su suka haɗe tana shaƙar ƙamshin sa, soyayyarsa na ƙara ninkuwa a zuciyarta, babu ɓata lokaci ta buɗe bakin ta ta haɗe da nashi ta soma socking tongue ɗin sa, Wani irin yanayi suka shiga domin sun ɗauki tsawon lokaci a wannan halin suna tsotson juna tamkar zasu mayar da junan su ciki Inda shi SHAREEF yake ta faman yamutsa ta yana sarrafa ta cikin yanayin halin fitan hayyaci, domin kamar ta san abun da yake yi wa zaƙwaɗi kenan ta taimaka masa But daƙyar ta ƙwace kanta a wurin sa sabida abun ya wuce tunaninta, Tana mayar da numfashi tare da kwantar da kanta a saman kafaɗansa ta riƙe hannunsa gam da yake ƙoƙarin ci gaba da abun da yake yi, Cike da shagwaɓa take cewa, "Please ka bar Ni haka ba na jin daɗi, ina son yin wanka in huta." Kasa magana yayi a time ɗin, sai dai bai ƙara yin mata komai ba ya soma mayar mata da rigan jikinta; tunda ya zame mata shi gaba ɗaya, sai da ya gyara mata before ya ɗauke ta cak zuwa cikin bedroom ɗin ta Da farko ta so ta hana sa abun da yayi ninya tunda yace, "shi zai mata wankan." But ta kasa hana shi sabida ya nane mata ya ƙi sauraron ta, Haka nan ta haƙura suka shiga cikin toilet ɗin. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 _____A yau sai ga su Haseena sun dira a ƙasan Nigeria, ita da Nana ta biyo ta Umma tayi mamakin ganin ta musamman da ta ganta da baƙuwa, kuma bata sanar musu da zuwan nata ba sai diran ta, Ga Abban su ba ya nan yayi tafiya ma a time ɗin, Ita dai hankalin ta bai kwanta da yanda ta ga Nanan ba, musamman yadda ta ga itama Haseenan irin ɗabi'arta ta koya duk ta ƙara canza wa, yanzu har da hujin baki, ga na hanci ga na baki, sannan ga sarƙan ƙafa ta saka, Sun yi wani irin shiga na ban mamaki tamkar wasu karuwai, Shiyasa koda suka shiga ɗakin Haseenan sai tayi kiran ta a waya ta sauko falo ta same ta, Tace, "wai Haseena ina kika samo wannan yarinyar da babu kyan gani a tattare da ita? Kuma ji be kema shigan da kika yi duk kin koma kalan ta? Anya ba ki manta al'adar ki na Bahaushe da kuma kasancewar ki Musulma ba?" Yatsina fuska tayi tace, "Umma, ki riƙa yin kyakkyawar zato don Allah, she's just my friend fa, tace zata biyo NI that's the reason da na taho da ita." Gyaɗa kanta Umma tayi before tace, "to shikenan, amma gaskiya hankalina bai kwanta da ita ba sabida yanda kika canza ɗabi'un ki Haseena, kar duniya ta zage mu a ce mun kasa ba ki tarbiyya, daga tura ki karatu kin zama wata iriya, idan Abbanki ya dawo ya ganki a haka ban san kuma mai zai ce ba Haseena." "Umma, wai kina zargina ne? Ni fa ban gane mai kike nufi da waɗannan zantukan naki ba? Just ki fito free ki faɗa min." Zata yi magana, sai ta hangi Nana tana sauko wa daga kan benen, Har ta sauya shiga zuwa ƙaramin wando da vest tamkar wani gidan Ubanta, ko ɗar babu a tattare da ita, Hakan ne yasa Umma bata yi magana ba ta zuba mata ido tana kallon ta da mamaki da jin abun da take cewa Tana kiran sunan Haseena da faɗin, "I'm hungry Babe, where's the food?" Sai Haseenan ta kalli Umma tace, "Mom, Honey tana jin yunwa, Allah yasa za a samu abinci a gidan?" "Eh akwai, ku hau kan dainng akwai abinci." "Ok, Honey zo mu je kan dainng." Haseenan ta furta tana miƙe wa tare da jiran Nanan ta iso wurin ta, Har da kama hannun juna suka sauya hira a tsakanin su suna dariya suka wuce wurin dainng ɗin Ita dai Umma abun ya bata mamaki musamman sunan da suke kiran junan su dashi, ga kuma alamun lesbian ya nuna a tattare dasu duk abun ya dame ta, ta san dai dole masu irin wancan ɗabi'an suke wannan sing ga junansu, ai yanzu kai ya waye kowa ya san da haka, musamman a yanda ta ga sun shaƙu ga kuma manne wa juna da suke yi, sai hakan ya ɗarsa mata zargi a kan hakan, Sai kallon su take yi ganin yanda har lokacin suna riƙe da juna suna zaune suna maganar da ba ta jin su suna dariya, Sai kuma daga baya ta ga Haseenan ta zuba musu abinci a plate ɗaya suna ba wa junan su, Hankalin Umma ya ƙara tashi gabanta sai faɗuwa yake yi, Miƙe wa tayi tabar wurin tana nufan hanyar kitchen, sai ta ɓoye tana leƙen su, Ta jima a wurin before ta hange su; Haseenan ta koma kan cinyar Nanan tana ɗibo abinci takai bakin ta, Tana zuba mata sai ta bi abincin ta haɗa da bakin ta da nata suka rungume juna, sai suka fara shafe-shafen juna kamar wasu mahaukata, Wani irin salati Umma ta saka jikinta na rawa, "yau na shiga uku na lalace! Mai zan gani haka? Kar dai a ce Haseena tana irin wannan mummunan rayuwar?" Jikinta sai rawa yake yi zuciyarta na hautsine wa tashin hankali yayi mata ƙawa, Fita tayi sabida ta ga halin da zasu shiga But sai ta ga ko a jikinsu, Sai ma Haseenan ce da ta ankare da ita sai ta janye jikinta tana miƙe wa ta koma mazaunin ta, ko sake kallon Umman bata yi ba, ga dukkan alamu kunya ne ya cika ta Umma ta tsaya tana bin su da kallo kamar zata cinye su, sai kuma ta juya zata bar wurin Da sauri Haseena tace, "Umma, wai yaushe Abba zai dawo ne? I missed him so much!" Juya wa tayi tana kallonsu, sai tayi yaƙe kawai tace, "zuwa gobe za ki gansa, ki kira sa a waya ai na san kun fi kusa, maybe ma ya dawo sabida ke." "Ok i will call him later, but yanzu zamu fita ne tare da Ƙawata akwai siyayyar da zamu yi." "Yanzu daga zuwan ku Haseena? Ki bari ku huta mana ko zuwa gobe ne." "A'a Mom, akwai abun da zamu yi ne shiyasa zamu fita." Kai kawai ta gyaɗa mata, sannan ta wuce zuwa ɗakin ta jikinta sai rawa yake yi sabida tashin hankalin abun da take gani, wai idanuwanta ne suke ganin karya ko kuma da gaske ne Haseena ne a haka? Anya abun da take zargin su dashi gaskiya ne? Wata zuciyar kuma ta kawo mata tunanin ƙila sabida wayewan su ne suke haka, itama Haseena ta je can ta saba da nasu al'adun shiyasa suka yi haka. Anya? Hankalin ta ya kasa kwanciya tana ji a jikinta dole akwai wani abu a tsakanin su, tabbas bata yarda da su ba akwai ayar tambaya, amma ko mene ne dole ta sanya musu ido ta ga abun da ke gudana a tattare da su, inyaso sai ta faɗa ma Abbanta su dauki mataki, domin kuwa in har haka ne tasu ta ƙare sun shiga uku sun lalace! Barin ƴarsu a wata ƙasa yin karatu bai musu rana ba, wannan ina zasu kai abun kunyar nan?. *** "Babe, why zamu fita yanzu? let us rest, I need you very much." A cewar Nana tana shafa face ɗin Haseena, sabida tun a lokacin da Umma ta wuce ita kuma ta koma saman jikinta, sai shafan juna suke yi Yayinda Haseena takai mata sumba tana lashe mata baki tace, "No, ki bari mu je mu dawo, hankalina bazai kwanta ba har sai na je wurin SHAREEF nayi abin da ya kawo Ni, ina buƙatar cire abun da ke raina." "Ok, but you will give me a chance today, because I really need you, ji nake yi kamar in cinye ki yanzu." Ta ƙare tana tsotse mata baki sosai; sai kuma ta koma tana lashe mata gefen kumatu tare da kafa mata haƙora cikin salo take sarrafa ta yanda zai yi mata dad'i Sai da suka gama jagula junan su before suka haƙura suka miƙe, Haseena ta je ta ɗauko wayanta tare da shiga ɗakin Umma ta amshi key din motanta, suka fita a tare Kai tsaye gidan su SHAREEF Haseena ta wuce da su, saboda bata san gidan sa ba don haka gidan iyayensa ta wuce, a nan bakin gate suka tsaya ta danna horn Mai gadi ya leƙo, sai tayi kiran shi tace mishi, "ya kira mata SHAREEF." Mai gadi yace, "ai babu SHAREEF a nan, yana gidan sa yayi aure." Yayi mata bayani batare da ya gane cewan Haseena bace tunda sau ɗaya ta taɓa zuwa gidan, so ko kaɗan bai gane face ɗin ta ba Ita kuma ta buƙaci yayi mata kwatancen gidan, Sai ya je ya kira driver tunda shi ya fi sanin gidan SHAREEF ɗin, kuma shi ya dinga kai wasu ƴan bikin lokacin da aka yi, Don haka shi ya basu address suka wuce suka tafi gidan SHAREEF A time ɗin SHAREEF har ya gama yin ma Maryamu wankan, don sai da suka ɓata lokaci a cikin toilet ɗin, abun da Maryamu ba ta so sai da ya faru domin ba ƙaramin kunyar sa bane ya sauko mata, Haka ta rafke mishi sosai kamar tana jin jiki ta dinga mishi kukan shagwaɓa; sannan ta samu kanta, Har suka iya wankan suka fito tare har shi, Kuma da kansa ya shirya ta ya saka mata wata doguwar Abaya fara mai taushi da kwalliyan jan zare a gaban, yayi mata kyau sosai rigan tunda tana da shape har da maɗaurin igiya a baya After ya gama saka mata kayan sannan ta saka hijab ta tayar da Sallah ta soma rama sallan da ya wuce ta Shi kuma sai ya wuce ɗakin sa zai canza kaya, sai da ya tsaya ya zaɓo wasu daga cikin kayansa ya zo ya jera su a wardrobe ɗin ta, A lokacin ne ya ji ƙaran bugun gate, Kuma bugun ba na wasa ba don an ƙi dena wa ana ta buga gate ɗin, Hakan ne yasa dole ya nemo riga ya saka mai ruwan madara t.shirt; da tambarin LJ a gaban da baƙin penti, Sai yayi saurin zura dogon wando a saman short trouser da ke jikinsa, Ya fita yabar Maryamu tana sallah a wurin har time ɗin bata idar ba, Kai tsaye fita yayi ya nufi bakin gate ɗin, sai da ya isa before ya tsaya yana faɗin, "waye ne?" Shiru an ƙi amsa mishi, ya sake tambaya ya ƙi ya buɗe ƙofan yana jiran jin amsa? But nan ma a cikin su babu wacce ta amsa mishi, Shi kuma sai ya ƙi buɗe wa yayi banza da su but yana tsaye a wurin soke da hannu a aljihu, Har zai juya sai kuma ya ji an yi magana, Nana ce tayi maganar that's why bai gane muryan ba, But hakan dai ya buɗe musu don ya ga su waye ne?. [02/05, 1:06 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE30* _____Idanunsa babu inda suka sauka sai kan Haseena da ke tsaye hannunta ɗaya rike da ƙugu, Zallan mamaki ne ya bayyana a kan face ɗin sa, wanda yasa ya kasa motsa wa illa bin su da kallo da yake yi yana mai tsananin mamakin ganin ta a nan ɗin Yayinda ita kuma Haseena ba ƙaramin yanayi ta shiga ba da yin tozali da Masoyinta, duk wani rashin mutuncin da ta kwaso domin ta sauke mishi sai ta ji ta nemi ƙwarin gwiwarta ta rasa, yayinda wani irin tsananin kewarsa ya mamaye ta, sai kuma mugun kyau da ya ƙara mata, musamman da ta ganshi ya rame sosai duk ya sauya mata, a idonta sai ya ƙara mata kyau ainun, wani sabon soyayyarsa ya turnuƙe ta, tana jin baza ta iya rayuwa babu shi ba, duk yanda za a yi sai ta same shi sai ta ɗauke kayanta Zungurin ta Nana tayi sabida ganin tayi shiru ta saki baki tana kallon SHAREEF Da shima itan yake kallo har lokacin, sai dai nasa kallon ya sha bamban da nata, mugun mamakin yanda ta sauya masa gaba ɗaya ta koma irin Nana yake yi, babu kyan gani a yanayin ta musamman matsatstsun kayan da ta sanya, ga kuma jan gashin da ke kanta uwa uba barima da ta saka a baki da hanci masu tsawo kamar wata Shanuwa, ƙyama ma ta ba shi daga ita har Nanan, sai yanzu yake iya ganin munin Haseena musamman a yanzu da tayi ƙiba na ban mamaki, tayi wani jawur kamar jini zai fita a jikinta, ko shi da yake mai hasken fata fiye da su, sai da ya disashe a gabansu, nan da nan ya soma yatsina face ɗin sa tamkar ya ga kashi, ganin sun tsaya mishi babu mai magana sai ya juya da ninyar rufe ƙofan Da sauri Haseena ta sanya hannu ta riƙe ƙofan tana shigo wa ciki, sai ta faɗa jikinsa da rawan jiki don ta kasa riƙe kanta, a yanda take jin matuƙar kewa da tsananin kaunarsa, ga shauƙin da ya kama ta, ita kanta bata san da cewan ga abun da ta aikata ba, Sai da ya ture ta da ƙarfi tayi taga-taga zata faɗi Yayinda Nana tayi saurin tare ta tana cewa, "babe, mene ne haka kuma? Are you a sense? You know what you are doing?" But kwata-kwata Haseena bata saurare ta ba, illa ma hankalin ta da ke kan SHAREEF tana kiran sunan sa Ya watsa mata wani kallo da tsananin ƙyamar ta a tattare dashi yace, "Enough don Allah, me ya kawo ki nan Please? Me kika zo min a gida?" "Dear, Ni ce fa, Haseenar ka, and kake tambayar mai ya kawo Ni gidan ka?" Haɗe fuska yayi sosai babu alamun fara'a a tare da shi, ya nuna musu hanya yace, "ku fitar min a gida Please tun kafin in yi muku rashin mutunci, already na tsinke igiyar aurenmu, there is no more relationship between us, I don't want to see you now, please leave my house." Idanunta sun kaɗa sun yi jazur sabida ganin wulaƙancin da SHAREEF yake musu, hakan ne yasa tace, "wlh baka isa ba SHAREEF, baka isa ka wulaƙanta Ni ba, zan ɗauki mataki a kanka sabida baza ka taɓa cin amanata ba, babu wata Macen da ta isa ta mallake ka bayan Ni, Ni ce Matarka kuma komai zan iya yi don ƙwace ka." Dariya ma ta ba shi, sai dai bai ce komai ba sabida ganin yanda Nana ta ja hannunta tana mata bala'i suka fice a cikin gidan, Sai ya mayar da ƙofan ya rufe yana jan tsaki tare da takaicin ta a tattare dashi, Kai tsaye cikin gidan ya nufa Yayinda Maryamu da ke tsaye a bakin window tana kallon su, duk da ba ta jin abun da suke furta wa, kishi ne ya cika ta ta kumbura suntum kamar zata fashe sabida ganin sa da wasu matan waɗanda bata tantance su waye ba, kuma bata jin abun da suke tattaunawa, Tana ganin ya nufo gidan sai ta koma saman gadon ta zauna, har yanzu da Hijabin da tayi sallah a jikinta, Kanta na ƙasa koda ta ji shigowar sa cikin ɗakin, Tana jin sanda ya zauna a gefen ta yana kamo hannunta, tare da sanya hannu ya ɗago haɓarta suna kallon juna Sai dai a yanda ya ganta fuskarta babu walwala tana masa wani irin kallo, sai hankalinsa ya ɗan tashi yake cewa, "what's wrong with you Baby? Me ya same ki kika sauya haka?" Hannu ta sanya ta cire nasa, tana zare ɗaya hannunta daga cikin nasa, idanunta a kansa tace, "su waye waɗannan suka shigo mana gida?" Mamakin tambayar nata yake, sai dai kuma ya gane halin da ta shiga sabida da su ne, sai kuma ya ji daɗi a ransa don ta nuna kishi a kansa, hannunsa ya sanya ya janyo ta jikinsa tare da sakar mata kiss a laɓɓa, kana ya haɗa goshin su wuri ɗaya cikin sanyin murya da tausasa wa yace, "Forget about these people, basu da amfani a waje na." Nan da nan sai ta shagwaɓe mishi kamar zata yi kuka tace, "to taya ya suka zo gidan nan? Ni ina son sanin su waye ne? Wurin ka suka zo kenan? Ka ga shigan da suka yi kamar arna." "Yes, wurina suka zo, Haseena ce." "Wace ce Haseena?" Ta tambaya batare da ta gane wacce yake magana a kai ba Shiru ya ɗan yi, sai kuma yace, "Matata wacce na aura." Cire face ɗin ta tayi daga nashi, tana bin shi da kallo kamar idanunta zasu faɗo ƙasa, yayinda ta tsuke fuska idaninta har sun tara ruwan hawaye, Amma ta kasa ɗauke ido a kansa sabida irin kallon da take watsa mishi Shi kansa jikinsa sai yayi sanyi, har hankalin sa ya soma tashi sabida ganin halin da ta shiga nan take ta ɗauke masa wuta, bazai so wani abun ya haɗa su ba kuma, don ita ce farin cikin sa a yanzu, don haka tuni ya kamo hannunta ya matse a cikin nasa sosai, ya tsira mata ido tare da faɗin, "ba abun da kike tunani bane Maryama, babu wata sauran alaƙa tsakanin mu da ita, already yanzu na sake ta don ban faɗa wa kowa bane, ban san da zuwan ta ba, kawai na je na duba ne na gansu that's the reason, but you are the only one in my mind now, because you are my happiness, I don't love anyone but you, so don't worry about anything bazan ɓata miki rai ba, You are my choose now, please smile at me." Wani irin daɗi ne ya cika ta, musamman da jin wannan sunan nata a bakin sa, sai ta ji daɗin sunan fiye da koyaushe, bata san sanda ta washe baki ba tsaban farin ciki, ga kuma kalman sakin da ta ji ya ambata, domin har ga Allah tana da zafin kishin da baza ta iya sharing SHAREEF da wani ba, irin tarin ƙaunar da take mishi baza ta iya jure ganin sa da wata bayan ita ba, don haka farin cikin ta ya kasa ɓoyuwa, tuni ta rungume sa ƙam tana dariya Shi kuma sai ya ji daɗin ganin yanda ta saki fuskarta, sai yayi amfani da wannan damar nasa nan da nan ya soma shafa ta sabida samun abun da yake so, musamman yanda ya ga ta ƙanƙame shi babu wani gardama, nan da nan sai kiɗan ya sauya suka koma mayar wa da junan su martanin soyayya. ***** _____Yayinda a wurin Haseena ba ƙaramin tashi hankalinta yayi ba, kuka ta saka lokacin da suka bar gidan don ta kasa riƙe tashin hankalin ta, wani sabon soyayyarsa ne ya dawo mata wanda tana jin baza ta iya hakura dashi ba, ta gummaci tayi masa abun da yake so in har bazai rabu da ita ba, baza ta taɓa barin sa da wata ba domin soyayyarsa ya zame mata jinin jikinta, SHAREEF wani ɓangare ne na rayuwarta, don haka da kukanta wi-wi take roƙon Nana ta taimaka mata Ita kuma takaici ya cika ta, nan fa ta dinga surfa mata bala'i tana cewa, "da ta san haka ne da tun farko bata biye mata sun zo nan ba, bayan alkawarin da tayi na barin sa har abada zata sadaukar dashi ga ƙungiya, amma yanzu ta sauya zance ta zaɓi wani a kanta? Tana son ta wulaƙanta ta ne." Haseena na kuka tace, "Honey, don't you understand, SHAREEF is my happiness, I will never be able to part with him, help me if you love me, I promise you that we will be together, I will never part with you, but ina son in ƙwace SHAREEF ya dawo wurina domin shi ne farin cikina, duk abun da kike so ina miki Please ki cika min wannan burin nawa, zama dashi bazai hana mu rayuwarmu ba amma shi nake so." Ganin da gaske take yi tana kuka sosai ta tayar da hankalin ta, shiyasa Nana ta sauko har ta bata tausayi sabida ba ta son abun da zai ɓata mata rai, tace mata, "yanzu mai take so a yi?" "Ina son in sake mallakar sa ya zama nawa Ni kaɗai, babu wata Macen da ta isa ta mallake sa bayan Ni, and I want to live with him. I can't go back to Australia, I will live with him because that is my happiness." "No, it is not possible, Haseena, you mean mun rabu; did you choose him over me? I cannot live there without you with Me" "Please help me with this, I can't go anywhere without SHAREEF with me, you have a chance to be near me but I won't go back there." "Well, we have a way to attract him to you, if he loves you, he will do anything for you, idan muka ɗauki mataki a kansa just ya biyo ki can kawai ku zauna tare, if not bazan yarda ba, kin san zan iya komai a kanki, ya rage naki." Haseena ta yarda da hakan shiyasa tace, "Ni komai za ki yi, ki yi in har zan same shi, burina mu zauna tare na raba shi da kowacce Mace, ita kuma wannan da ta shiga tsakanin mu ba na son sake ganin ta a doron ƙasa, domin tunda ta haɗa hanya dani ta riga Ni mallakar sa sai na ɗauki mummunar mataki a kanta." Killer smile Nana ta saki, tace, "good, I will do whatever you want, just put it in your heart and from now on, you don't have any problem, let's just go." Tuƙa motan Haseena tayi after ta share hawayen fuskarta, yayinda suka koma gida daga nan. ***** Shi kuma SHAREEF, yana samun time ya kira Dady ya faɗa masa abun da ke faruwa, already ya faɗa masa, "ya saki Haseena yanzu sun rabu, bazai iya ci gaba da zaman da igiyar auren ta ba." Shi kansa Dady hakan ya fi so, tunda ba amfanin zaman nasu, yace mishi, "Allah yasa hakan shi ya fi alkhairi, zai faɗa ma Momyn su, sannan shi da kansa zai kira Mahaifin Yarinyar ya sanar musu." Koda Momy ta ji zancen ta fi kowa farin ciki, don babu wanda yakaita murnan ganin SHAREEF ya rabu da Haseena, tun farko bata so auren ba, kuma da abun ya zo da matsala rabuwar shi ya fi alkhairi a yanzu, don haka basu tashi hankalin su ba, suna fatan a ce wannan shi ne zai zama sanadin zaman su lafiya shi da Maryamu Shima Dady ɗaukan waya yayi ya kira Abban Haseena, ya zayyane masa abun da ke faruwa, a cewar sa, "tunda yarinyar ta nuna baza ta zauna dashi ba, rabuwar ita ce mafi alkhairi, in ta samu wani Mijin tayi aure kawai." Sannan ya basa haƙuri daga ƙarshe ya nuna masa, "ba haka suka so ba, amma yanda Allah ya tsara ne." Ko kusa Abba bai ji haushi ba, tunda a ganin sa don SHAREEF ya rabu da ƴarsa ai ba faɗuwa suka yi ba, zata samu wanda ya fi shi, dama don ita Haseenan ta matsa dole sai shi ne, kuma shi abun da take so shi yake so, don haka bai damu ba sam suka yi sallama daga nan, Shima ɗin sai ya kira Umma ya sanar mata tunda ba ya gidan, sai gobe zai dawo Umma hankalin ta ya tashi matuƙa, don wlh bata so hakan ba, tun farko ta so Haseena ta zauna a ɗakin Mijinta don haka ya fi mata alkhairi ko don ta tsira da mutuncinta, kuma suna bukatar ganin jikokin su tunda ta kawo kai yakamata a ce a yanzu tana ɗakin Miji da Yaranta, karatu ne dai tayi iya yin ta ya isa haka, abun yayi mata ciwo musamman yanzu da ta soma zargin su da Nana, hankalin ta a tashe yake, A nan take sanar mishi, "Haseenan ma tana gida, ta kira sa ta faɗa mishi?" Abba yayi mamaki yace, "no bata faɗa min ba." "Ai kuwa tun safe ta dira a ƙasan, ita da wata ƙawarta suka zo." "But shi ne ba ki sanar min ba?" "Alhaji na sha'afa ne, kuma nayi tunanin kun yi waya ne tunda nace ta kira ka." "Ok ki kashe wayan bari in kira ta muyi magana." Amsa mishi Umman tayi sannan ta kashe wayan, Sai can kuma ta sake jin kiran nasa Bayan ta ɗauka yake cewa, "ya kira wayan but bata yi peaking ba, ta bata wayan yanzu su gaisa." "To bari dai in kai mata, sabida yanzu Ni ina falo ne tana ɗakin ta, ina zuwa bari in kai mata." Ta miƙe ta nufi ɗakin Haseenan riƙe da wayan a hannu While su kuma su Haseena suna ɗakin hankalinsu yayi gaba wurin biya wa juna buƙata, wayan tana vibration bata san ma ana kira ba, sun yi nisa a harkan nasu haihuwar Uwayen su. [02/05, 1:25 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE31* _____Ba ƙaramin tashin hankali ne ya riski Umma ba; a lokacin da ta shiga ɗakin Haseena ta gansu a wannan yanayin mummunar yanayin da ya hautsina mata ƙwaƙwalwa, take a nan ta saki wayan a ƙasa ta kwatsa ihu, kana salati ya biyo baya jikinta na faman rawa hannayenta a saman baki Yayinda su kuma tuni sun dawo a cikin hayyacinsu, inda Nana tayi saurin ɗaga Haseena wacce take kwance malale a saman gadon tsirara daga ita har Nanan, Babu wacce ta kuma motsi a cikin su don basu da sauran kuma abun da yakamata suyi Umma kuma ta kasa ɗaga kafanta bare ta tafi sai bin su da kallo take yi, gabanta na buga wa da ƙarfi tashin hankali ya bayyana a gaba ɗaya fuskarta, har lokacin salati take yi tana jin kamar mafarki take yi, wai yau ƴarta ta kama hand right da wata Macen suna aikata masha'a, bama namiji ba wai Mace? Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Wannan wanne irin bala'i ne? Mai duniya ta zama haka? Ranta yayi matuƙar ɓaci da nan take ta fashe da kuka tana nuna inda Haseenan take, Wacce a yanzu ta tashi zaune tana neman riganta zata rufe jikinta, cikin tsawa da tashin hankali take cewa, "Haseena, ke ce yau na kama da wata kuke aikata saɓon Allah irin haka? Wanne irin bala'i kike son jawo mana a gidan nan? Wanne irin abun kunya ne wannan? Mai muka rage ki dashi da har kika amince ki ci amanarmu ki saɓa mana a kan tarbiyyar da muka yi miki? Haseena..." Sai tayi shiru ta kasa ƙarisa zancen sabida ɗacin da ya ziyarce ta da takaicin abun da ta gani Ita kuma Haseena rigan ta gama sanya wa tana kallon Nana da ko a jikinta, ita kanta bata wani damu ba tunda aikin gama ya gama, don haka cikin borin kunya tace, "Umma, ki yi hakuri don Allah kar ki sanar da Abba abun da kika ga muna yi, sharrin shaiɗan ne wlh, kuma bazan sake ba daga yau baza ki sake ganin na aikata ba, amma ki yi haƙuri." Jinjina kanta kawai tayi ta kasa magana, sabida har lokacin baƙin ciki da ɓacin ran da take ji ya hana ta sake buɗe baki, har ta juya zata fita sai kuma ta sake dawowa tana kallon Nana a fusace tace, "zo ki wuce don kutumar kan ubanki ki bar mana gida, shegiya asararriya gantalalliya, duk yadda aka yi ke kika ɓata mana yarinya kuma baza mu taɓa yafe miki ba, ki zo ki wuce nace." Ta daka mata tsawa mai firgitar wa Sai Haseena tayi saurin cewa, "Umma a kan me zata tafi wani wurin a wannan tsohon daren? Ita fa baƙuwata ce, in har tabar gidan nan to tare zamu bar gidan but babu inda zata je." Zuciya ce ta ɗibi Umma tsaban ɓacin ran maganganun Haseenan, ta nufe ta da sauri ta janyo ta ta soma jibga tana cewa, "Ni za ki gaya wa magana irin haka don ubanki? Au don ba ki da hankali ina cewa tabar gidan kike maganar za ki bi ta? Kashe ki kawai zan yi in huta domin baza ki jawo mana abun kunya ba Haseena." Wani mari takai mata; amma sai Nana ta tare ta tana ture ta ta faɗi a ƙasa, cike da isa da taƙama tace, "Mom kar ki sake taɓa ta cus zan dauki mataki a kan hakan, bazan iya jura ba." Sai ta mayar da hankalinta kan Haseena tana rarrashinta har da shafa mata fuska before ta sumbace ta tana rungume ta Umma fa hankalinta ya ƙara tashi, ganin baza ta iya jure wa ba sai ta miƙe ta fita da saurin ta, kai tsaye kitchen ta nufa ta ɗauko muciya ta dawo babu zato tahau kansu da duka su dukka, Haka take zagin su tana cewa, "yau zata yi maganin iskancin su, sai tayi ajalin su gaba ɗaya, da dai Haseena ta jawo mata abun kunya gwara ta kashe su ta huta." Daƙyar suka ƙwace muciyan, Haseena da kanta ta ture Umman don ranta ya ɓaci sabida abun da tayi musu, musamman haɗa su da tayi ta duka, cikin rashin kunya da fetsarewan ido tace, "wlh Umma sai kin biya dukan nan da kika yi, bazan yafe ba tunda ban miki komai ba, ai rayuwata ce Ni naga zan iya abun da nayi ninya, ina da ƴanci duk abun da nake so, haka kawai ki kama dukan mu?" "Haseena Ni kike faɗa wa haka?" "Eh Umma na faɗa ɗin, baza ki hana Ni abun da nayi ninya ba, a kan Honey zan iya yin komene, don ba ki san yadda muke da ita bane, don Allah ki fice a ɗakin nan tun kafin in miki mummunar rauni." Cikin ɓacin rai itama Nana tace, "Babe abun da wannan Matar tayi min ba a taɓa min a rayuwata ba, idan ba ki ɗauki mataki ba Ni zan ɗauka, because I will never let her go." "I don't care what you want to do to her, I won't say anything." Haseena tafaɗa tana cika tana batse wa Kuka Umma ta saka abun takaici ya ishe ta, yau ƴar cikinta ne take mata wannan rashin kunya haka? Mai suka aikata wa Allah da ya jarrabe su da wannan iftila'in? Tabbas wannan mummunar rana ne da baƙin ciki zai kashe ta, yadda zuciyarta ke mata zafi ta kasa tsayuwa tana shirin faɗuwa, sai ta juya tana kuka ta nufi hanyar fita, har ta buɗe kofan kuma ta juya tace, "Haseena wanne irin laifi muka aikata miki da kika saka mana da wannan mummunar hukuncin? Shikenan bari Abbanki ya dawo tunda Ni na kasa ɗaukar mataki a kanki, in har mu muka haife ki ke jinin mu ne mu'amalar ki da wannan yarinyar in har ba ki datse shi daga nan ba; Allah ya isa ban yafe miki ba, kuma za ki ga mai zan yi akai." Ta fita batare da ta ɗauki wayanta da ta sake ta tun shigowarta na farko ba Haseena kuwa ko a jikinta ta rufe musu ƙofa ta koma tahau ba Nana haƙuri; sabida ganin ranta ya ɓaci sosai Nana tace, "kin san bazai yiwu mu bari ta fallasa mana asiri ba ko? Domin a cikin secret ɗin mu babu buƙatar a san mai muke aikata wa, hakan yana jawo wa ƙungiya matsala gagaruma, We don't think she knows this, so we have to take action." Haseena was silent, then she said, "What do you mean now?" Kallonta tayi, sai tace, "You know, what we should do, otherwise she will reveal the secret to us, and it will not be possible for anyone to hear more." Ita kanta Haseena ta san da haka, tunda a yanzu ta fahimci cewa tun farko neman da Nana tayi mata duk cikon aikin ƙungiya ne, dole sai suna neman junan su, kuma hakan shine babban sirrin su wanda shi ke kawo musu ci gaba sosai a ƙungiya, ta hakan ne suke samun kuɗi da kuma ƙarfin tsafin su, babu daman su fasa wannan harkan, duk wanda yake ciki yana mu'amala da ko waye in har ya kwanta musu a rai, kuma a duk karshen wata ana samo yara irin ƙanana Ogan su yana amfani da su a kashe su sannan a sha jinin su, duk wannnan sirrin su ne, shiyasa ɓatan yara yake yawa sosai a duniya, don ko ina suna samo Yara domin cikan burin su, sannan idan suna aikata wannan harkan wani ya gansu hakan na ƙara rage wa ƙungiyar su ƙarfi, kuma abun na tasiri su samu matsala har asirin su ya tonu, shiyasa duk wanda ya gani hukuncin sa kawai kisa ne batare da sun bari ya sanar da wani ba; bare asirin su ya daɗa bayyana ga jama'a, So Haseena ta san da haka, duk da sonta da Mahaifiyarta bata da wannan damar da zata hana a kashe mata Uwa, don ta san ko sun bar ta ita kuma Umma baza tayi shiru ba, sannan ƙungiya zata san da haka tunda zasu soma ganin matsaloli. *** Umma bayan ta koma ɗaki sai ta nemi wayanta ta rasa, ta so a lokacin ta kira Abba ta faɗa masa, tuna inda tabar wayan sai tayi zaman ta a gefen gado tana ci gaba da matse hawaye, abun duniya ya bi ya ishe ta gani take yi kamar an sauya musu Haseenan su, Haseena baza ta taɓa yin abun da wannan tayi ba, lallai kam tura ƴarsu wata ƙasa bai musu amfani ba tunda ta kwaso abubuwan da ba a san ɗan musulmi dashi ba, abun ma ya fi ƙarfin ta wai lesbian Mace da Mace, innalillahi wa'inna ilaihi raji'un...! Wannan wanne irin bala'i ne? Wanne irin kuskure suka aikata haka? Tabbas akwai laifin su amma dole ne su ɗauki mataki, mummunar mataki kuwa, domin tseratar da ƴarsu, Don haka ta miƙe ta shiga toilet zata ɗaura alwalan sallan isha'i da bata yi ba, Ga dare yayi amma ba don haka ba da ta fita; koda Uncle ɗin su ne ta sanar dashi, amma kuma da tayi tunani sai ta ga maganar ba na sanar wa jama'a bane, domin su zasu kwana a ciki tunda idan maganar ta yaɗu sun shiga uku, abun kunya ne wannan Ta shiga toilet tana cikin alwalan ne, ta gama kama ruwa tana wanke hannu, sai ta ji cikinta ya murɗa, kamar wasa kuma abun ya soma fin ƙarfin ta, dole ta dakata ta riƙe cikin nata gam tana salati da sallallami, Kafin wani lokaci jikin Umma ya ɗau zafi sai karkarwa take yi nan da nan ta zube ƙasa don ƙafafuwan ta sun gaza ɗaukar ta, Kamar an ɗaure ta haka take ji; daga nan kuma sai numfashinta ya ɗauke abun kamar a mafarki ta tsinci kanta a wani baƙon wuri da ta kasa gane mai ke faruwa da ita, duniyar ta juya mata ta zamar mata sabuwa sai ganin wasu jajayen abubuwa take yi da ta kasa gane mene ne, Jima wa kaɗan kuma sai ta soma jin maganganu but ba ta fayyace maganganun su waye, kuma bata san mai ake faɗa ba, tamkar an ɗaure ta komai nata ta kasa motsi dashi, kamar kanta ma a ƙasa yake ƙafafunta a sama shiyasa ba ta iya tantance mutanen wurin, Sai kuma daga baya ta soma jin murya kamar na Haseena a kusa da ita, Natsuwa tayi sosai ta tsayar da zuciyarta daga tsananin tsoron da ya addabe ta, domin tantance muryan Haseenan, don zak irin muryan take ji "Umma, bani da yadda zan yi ne dole ne ta sa hakan, kin gano abun da ya fi ƙarfin ki, nima haka bazan iya taimaka miki ba, amma ina baƙin cikin ganin wannan rana da nayi sanadiyyar mutuwarki da ke da ƴar uwata Haajara." Laɓɓan Umma suna motsi tana son yin magana amma ta kasa, komai na jikinta kamar ya saki ne baza ta taɓa iya amfani dashi ba, kuma sarai ta gama jin zantukan Haseenan da ke fitar mata bibbiyu amma ta gaza gane inda maganar ta dosa, to wai shin aina take ne? Daga shiga toilet kuma sai hakan ya kasance da ita? Mai ke shirin faruwa da ita ne? Daga ƙarshe maganganu sun sake yin yawa ta kasa bambance mai ke faruwa, sai kuma ta ji kamar an ɗaura mata abu a cikinta, kamar kuma ya lume ne, a hankali ta soma ganin jini na ɓulɓulo wa ta hancin ta da bakin ta, kafin ta tantance mai ke faruwa rai yayi halin sa Sai da suka gama tsaface-tsafacen su before a dawo da gawan nata a cikin ɗakin nata, Inda Haseena babu ko nadamar abun da ta aikata, domin zuciyarta a ƙeƙashe take musamman tun lokacin da ta fara shan jinin ƴar uwanta, bare yanzu kuma jinin mahaifiyarta shima ya shiga jikinta da ƙarfin tsafi, hakan yasa zuciyarta ta ƙara tauri babu wani ɓurɓushin imani, Ita da kanta ma ta kira Abbanta ta zayyane mishi halin da ake ciki, bayan ta nuna tashin hankalin ta da kukan da ta saka mishi na ƙarya, ta faɗa mishi, "Umman bata da lafiya ta faɗi a ƙasa babu numfashi a tattare da ita." Ba ƙaramin tashi hankalin Abba yayi ba, ya ruɗe gaba ɗaya yace mata, "tayi maza ta kaita asibiti. Ta ɗauki driver ya kaisu asibiti shima a daren nan zai dawo." Bayan ya kashe wayan sai ya kira ƙaninsa ya sanar masa halin da ake ciki domin ya bi bayansu Sabida iya taku shiyasa Haseena ta ɗauki Umma da taimakon Nana, suka tafi da ita asibiti, A can ne Uncle ɗin su ya je ya tarar da su, Ko lokacin Likitoci sun gama binciken su sun gano rai yayi halin sa, tunda tuni ta shura, sai dai basu gane takamaiman abun da ke faruwa da ita ba, kawai dai sun ɗaura zargin su a kan jinin da ta zubar ne har hakan yasa ta rasa ranta Tashin hankali dai ba a sa mishi rana, kowa ya ji mutuwar Umma amma ban da Haseena da ta dinga pretending, tun a ranan Abba ya dawo shi kansa yayi kuka sosai, don mutuwar tayi musu diran mikiya ce basu taɓa tunanin hakan ba, babu zato babu tsammani, ga shi mutuwar iri ɗaya dana Haajara duk yanayin abun da ya kashe su kenan, Sai dai babu hujja bare a yi zargin wani abu Har washe gari haka mutane suka yi ta cika gidan, a ranan ma aka yi jana'izar ta, Yayinda ƴan uwa da Abokan arziki suka ci gaba da zaman makoki Gefe ɗaya kuwa, Nana da Haseena ba abun da ya shalle su, suna dai iya takun su amma ko'ina tare suke kamar tif da taya, A yanda Haseena ta tashi hankalinta ta damu da tunanin SHAREEF, ko kusa bata damu da mutuwar Umma ba, don yanzu SHAREEF shi ne burin ta a yanzu, bata da burin da ya wuce su samo kansa ya dawo gare ta Yadda ta damu shiyasa Nana ta amince mata suka soma daukar mataki, suka fara aiki a kansa. [04/05, 5:53 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE32* _____Maryamu tsab ta warke sabida kulawar da take samu a wurin SHAREEF, kulawar da bata taɓa tunanin samu ba, dama har da sabon al'amarin da ya gudana a tsakanin su ne, ga kuma abun da ya faru a ranan na tsoratan da tayi, dalilin da yasa zazzafan zazzaɓin ya cafke ta kenan, but lokaci ɗaya komai ya sauya sabida samun kulawa da tattali a wurin SHAREEF, ga wani irin soyayya da yake nuna mata mai tsaya wa a rai, takan manta dukkan wani baƙin ciki idan suna tare, a yanzu ba ƙaramin farin ciki take samu ba, Don shi kansa ya san cewa yayi sabon aure, lokaci guda ya soma jin rayuwarsa ta sauya fiye da tunanin sa, sabida a yanzu yana tare da wacce take matuƙar ƙaunarsa suna ba juna kulawa fiye da tunani, garɗi da madaran soyayyar da suke shayar da junan su, sai suka ji tamkar su dauwama a haka, ko kuma su kaɗai ne a duniyar babu kowa A yanda SHAREEF yake samun kulawa wurin Maryamu har ya sauya a cikin ƙanƙanin lokaci, don har Kumari yayi ɗan raman nan ya kufce masa, wuni yana liƙe da ita kamar chewing gum ba ya barin ta ta sarara ko na minti ɗaya, a takaice ma ko samun damar yin girki ko wani gyaran gida ba ya barin ta suyi, idan suka ƙule a ɗaki suna manne a saman gado yunwa kaɗai ke fito da su, To sai a lokacin ne zai ƙoƙarta ya fita da sauri yayi musu take away, wani lokacin ma sai dai su sha tea A sanda ya fita shine zata samu ta ɗan gyara gidan before ya dawo don ta san bazai barta ta huta ba, abun har ya soma gundiran ta sabida rashin sabo da kuma naci irin na Bawa, sai dai a yadda take ƙaunarsa ba ta iya mishi musu ko kaɗan, duk abun da yace tayi tana masa don ta faranta mishi rai, tana ganin kamar wannan dama ce da ta samu da ba kowacce Mace bace zata samu irin sa, a kullum tana godiya ga Allah da ya mallaka mata farin cikin ruhin ta, don irin farin cikin da take ciki baki ma bazai iya misaltawa ba, kuma a yanda suka samu kusanci hakan zai sa soyayyarta ta ƙara cusuwa a zuciyarsa kamar yanda itama ta mutu a ƙaunarsa Yau ma suna manne a tare, duk wunin yau babu inda suka fita ko falo, bare dama har yanzu su SHAREEF basu koma hutun da suka ɗauka na wurin aiki ba, Gwara ma Hanif kwana biyu yana leƙa wa da yamma, Amma SHAREEF tunda ya samu abun da yake so sai ya manta komai, Maryamu kaɗai yake iya gani a idanunsa, ko kaɗan ba ya iya ɗaga mata ƙafa sabida tsaban jaraba da tsananin muradin ta, sai yanzu ya sake tabbar da wautan sa da kuma kuskuren da ya aikata a baya, da tun farko ya yarda da auren ta da tuni komai ya wuce, Yanda yake jin ta a zuciya ba irin yanda yake jin kowacce Mace a zuciya bace, duk da mutum ɗaya ya taɓa so amma yana jin ya soma shan bamban dana Haseena, tunda ko misƙala zarratan ba ya son ya jirga a kusa da ita, burinsa kawai su kasance a tare su dauwama a haka sabida nishaɗin da yake samu Amma kuma abun da ke faruwa yanda ya soma jin tunanin Haseena na dawo masa a ransa, har faɗuwar gaba yake fama dashi kwata-kwata sai ya ji farin cikin sa na son kufce masa, Suna kwance a kan gado ya rungume Maryamu a jikinsa, sun rufe jikinsu da blanket Inda ta ɗaura kanta a saman ƙirjinsa har barci ya soma kwashe ta sabida samun hutun da tayi, shiyasa ta ɗan soma gyangyaɗa wa before ya tayar da ita da jarabar sa, Har barcin ta ya soma nisa bata ji ya tashe ta ba, sai ta kara gyara kwanciyarta nan da nan barcin ya fizge ta har da ɗan munsharin ta Hakan ne yasa SHAREEF jin tana damunsa kasancewar yanda yake bukatar natsuwar zuciya da tunanin da ya bijiro masa, Kasa haƙura yayi; sai ya lallaɓa ya janye ta a jikinsa ya sauka daga kan gadon, rigansa ya ɗauka ya zura a jikinsa before ya fita falo yayi zaman sa a can, duk yanda ya so ya janye daga wannan tunanin da ke faman addabar sa kamar ana ƙara huro masa wuta, amma ya gaza don tunanin ya soma cin ƙarfin sa, har yana jin kamar sabon soyayyar Haseena ce a zuciyarsa ke son azalzalan sa, kuma ga mararin ganin ta da yake bukata, Tuna lokacin baya da yanda ya sha fama da wahalhalun soyayyarta, da kuma shawaran da Hanif ya basa har ya samu sauƙi, shiyasa ya soma ƙoƙarin karanto addu'o'i a ransa, amma hakan ya gagara, sai ya kama kuma sai ya saki, tsaki ya dinga ja sai kuma ya tashi ya nufi saman dainng ya haɗa tea mai kauri ya shanye, yana sha yana faman tunani ya dafe kansa da hannu ɗaya, Daga ƙarshe kuma bayan ya gama sai ya miƙe ya koma ɗakin sa, ko kallon inda Maryamu take kwance bai yi ba, ya shige toilet ya faɗa wanka sannan ya fito ya shirya cikin ƙananun kaya, mai ruwan ƙwan riga wacce ta matse shi tayi masa kyau ainun, sannan ya sanya blue jeans tare da combat din sa shima blue, tsab ya fito yayi kyau cikin kwalliyan da yayi, sai ya feshe ko'ina nashi da turarukan sa masu shegen ƙamshi da fizgar hankali, Daga nan ya fice after ya ɗauki mukullin mota da wayansa, ya fita ya ɗauki motansa yabar gidan tare da nufan gidan su Haseena, don yana ji a ransa idan bai je ya ganta koda sau ɗaya bane komai zai iya faruwa, yana fatan ace tana nan bata bar ƙasan ba; since ya ji labarin mutuwar Mahaifiyarta maybe tana nan bata tafi ba Inda fitan sa ke da wuya Maryamu ta farka, sabida a ɗan firgice take gaba ɗaya yanayin nata ba ta jin daɗi, wani irin ƙuncin zuciya take fama dashi, yayinda nan da nan kanta ya soma sara mata, musamman da ta buɗe ido ta soma jin ƙamshin turaren SHAREEF ya cika mata hanci sosai, sai ta ji ranta ya soma ɓaci kamar zata yi amai, saurin rufe hancinta tayi tana sake laluba kan gadon jin da tayi kamar babu kowa, Ta sha mamakin rashin ganinsa, but sai tayi shiru tana tunanin maybe yana toilet ne, amma ganin har lokaci ya ɗan soma ja dole ta miƙe tana dafe da kanta da ke faman sara mata, ji tayi baza ta iya ci gaba da zama a ɗakin ba, shiyasa sai ta ɗauki yaloluwar rigan barcin ta ta fice daƙyar take tafiya, A falo ma babu kowa, but sai ta tsaya tana kiran sunan sa tana mamakin ina ya shiga, har kitchen ta leƙa bata ganshi ba, Bakin window ta nufa ta leƙa sai ta ga babu Motansa ɗaya a wurin, hakan ya tabbatar mata da ba ya gidan kacokan, Dole yasa ta koma ɗakinta amma tana mamakin inda ya je, bata wani tsauwala ba sabida barcin da ke damun ta, ga kuma ciwon kan da ke mata barazana tana jin duk babu daɗi a tattare da ita, kwanciya tayi ta rufe kanta da blanket but ta gaza yin barci, abu kamar wasa ciwon yana ƙara daɗuwa mata, wani irin ciwon kai ne ke kawo mata cafka ga faɗuwar gaba zuciyarta sai buga wa take yi, Tun tana jin abun da wasa sai kuma abun ya fara cin ƙarfin ta, lokaci guda ta soma fita a hayyacinta manyan idanuwanta sun ƙara buɗewa sun yi wani irin ja kamar zasu fito, A hankali ta soma sakin kuka tana murkususu kamar wacce hankalinta ya gushe, Sai ta soma ganin ɗakin ya soma canza mata kala kamar ya koma daji-daji, amma bata da ƙarfin addu'a yayinda gaba ɗaya yanayin ta ya gama sauya wa Wata ƙatuwar Kunama ne ta faɗo a saman gadon, ƙatuwa ce mai narkeken kai da baƙin jiki, lokaci ɗaya ta ɗana Kunamar ta zata kai mata sara Allah da ikonsa sai Maryamu ta buɗe idanunta ta sauke akan Kunaman nan, ko kafin takai mata saran tuni ta faɗo tim a saman gadon, A haukace ta miƙe zata bar ɗakin batare da ta san inda hankalin ta ke jikinta ba, sai dai kamar ana ingiza ta ne zuwa Kofar fita Yayinda Kunamar tuni ta bi bayanta ko kafin ta fita ta ɗana mata ƙarin ta a ƙafa Ihu ta yanka ta faɗi a nan ƙasa tana shure-shure idanunta sun sake fitowa waje kamar an zuba musu barkono, Haka Kunaman nan ta sake samun dama ta sakar mata wani ƙarin daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba, kamar an yi ruwa an ɗauke numfashin ta ya ɗauke daga gangan jikinta Ƙara Kunaman ta saka mai kama dana Mutum, daga nan kuma ta ɓace ɓat sai ga ta ta rikiɗe ta koma Haseena tana ɓaɓɓaka dariya sabida farin cikin samun nasaran kashe Maryamu, Shikenan matsalarta takau Da sauri Nana ta rungume ta tana tambayarta yanda tayi ta kashe Maryamun? Cikin farin ciki Haseena ta bata labarin komai tana dariya, sai tace, "yanzu Burina ya kusa cika, na tabbata duk taurin kan SHAREEF sai ya dawo gare Ni, domin a yanzu haka ma aikin mu ya fara tasiri fiye da koyaushe yana nan zuwa nan gidan." Ko kafin ta dire maganarta sai suka soma jin hayaniya kamar na muryan Abba a waje Jin abun da yake faɗa shine dalilin da yasa Haseena ta miƙe ta duba window, ta hange sa tsaye tare da SHAREEF yana ci masa mutunci sabida ganin sa a gidan sa; after ya sakar masa ƴarsa, Da sauri ta fice a ɗakin ta fita wajen, "Abba." Ta kisa sunan sa da sauri tana ƙarisa wa inda suke While Nana tana tsaye a bakin ƙofan tana kallon abun da ke faruwa Kai tsaye wurin ta ƙarisa batare da kunyar Abba ba ta rungume shi cikin tsantsan farin ciki Shi kuma kamar soko haka ya tsaya sai ma farin cikin da ya ji yana ziyartan sa sakamakon tozali da ita da yayi, nan da nan ya sanya hannu ya sake manna ta a jikinsa Abba da baki a sake ya bi su da kallo kamar ya samu TV, sai kuma yace, "Haseena, mene ne haka kike yi? A gabana kike rungumar wanda ba Mijinki ba?" Ɗago kai tayi tana duban Abban, sai tace, "Abba wa yace maka ba Mijina bane shi? I love him so much, ka bari zamu tattauna dashi and I will tell you everything, please give us another chance." Shiru Abba yayi, but sai da yayi wa SHAREEF wani kallo before yace, "okay, amma ki kula daughter." Daga haka ya juya yabar wurin ya shige cikin gidan Ita kuma sai tayi ɗage ta sumbace shi saboda rashin takalma a ƙafanta, daga nan ta ja hannunsa tace, "mu shiga ciki." Haka ya bi ta kamar jela babu musu a ransa, amma kuma yana tunanin abun da ya aikata anya ya dace kuwa? Mai zai sa ya ji yana sonta a yanzu after sun rabu? Mai ke shirin faruwa dashi ne? Cikin falon suka shiga suka zauna a saman two sitter, inda ta manne dashi tana ɗaura kanta a kafaɗansa sabida kewarsa da tayi, yayinda take jin soyayyarsa na ƙara tasiri a zuciyarta, tabbas baza ta iya barin ma wata ɗiya Mace shi ba, ya rigada ya koyar da ita Zumar soyayyarsa, SHAREEF ba irin Mazan nan bane da ake samu cikin sauƙi ba, ire-iren su cikin ƙasar nan namu suna da ƙaranci, komai ya haɗa wanda ɗiya Mace mai ji da kanta zata mutu a ƙaunarsa, Tuni ta ɗago kanta suna kallon juna, sai takai fuskarta zuwa ga nasa tana shirin haɗe bakin su wuri ɗaya Tuni ya buɗe nasa bakin ya shigar dashi cikin nata sun soma tsotson juna cike da shauƙin so, wani irin yanayi suka shiga gaba ɗayan su musamman yanda take mishi irin salo tana shashshafa shi kamar zata haɗiye shi, nan da nan ta ci nasaran zautar dashi ya biye mata sun zama kamar chewing gum a wurin Tsawon lokaci suna a wannan yanayin, before su dakatar da abun da suke yi, yayinda fuskarta ke kusan nasa take shafa kafaɗansa cikin salo tana faɗin, "dear, meyasa kayi min haka don Allah? Ka san fa ina son ka da yawa, Please ka dawo da soyayyata a cikin zuciyarka mu dawo mu kasance tare, i love You so much and bazan iya rayuwa babu kai ba, Please." Gaba ɗaya ta kashe masa jiki musamman yanda take maganar cikin tsantsan shagwaɓa da karya murya, lokaci ɗaya tayi tasiri a kansa sabida har lokacin tamkar bai san mai ke damun sa bane, don haka ba shi da wani zaɓi face ya kyautata wa zuciyarsa sabida muradin ta da take yi, nan ya buɗe baki yana bata haƙuri a kan abun da yayi mata, sannan ya ƙara da faɗin, "i love You too sweetheart, idan kin yarda zan mayar da ke dakina domin mu kasance tare, I will give you everything you want but now I need you in my life." Daɗi ne kamar ya kashe ta sabida ganin ta ci nasara, "But if you love me, can you give me everything I need?" "Yes, Whatever you want, I will give it to you, ki faɗa whatever you want." Cikin kissa da karya murya tana ƙara danna mishi ƙirjinta tare da goga mishi cikin salo take cewa, "but ka ce min kana da wata Matar, Ni kuma bazan iya zama da wata ba, idan kana son farin cikina domin mu kasance tare dole Ni kaɗai zaka zauna da Ni, domin Ni kaɗai na cancanta da kai, dani kaɗai ka dace dear, and ina son ka bi Ni Australia mu zauna a can mu ji daɗin rayuwarmu tare, if you do this for me and finish everything for me, I will believe you very much, and I will love you more than anything in the world." Shiru SHAREEF yayi ya kasa cewa komai sabida jin abun da tace, but ba ya tunanin zai iya yin hakan, don haka ya kasa magana yana tunani a ransa While ita kuma sai ta tsira mishi ido tana jiran amsar shi, ta san idan ta ci galaba a kansa shikenan ya zama nata na har abada, don haka sai tayi amfani da damarta ta miƙe tace masa, "tana zuwa." Daga nan ta tashi ta je ta amso drink ɗin da suka haɗa domin shi, don in ya sha shikenan kuma soyayyarta zai dawo fiye da kowa a duniya, komai tace yayi zai yi mata, Tana zuwa ta miƙa masa cikin kwarkwasa tace mishi, "ya sha kawai, koyaushe zai iya bata amsa but ba sai yanzu ba, zasu sake magana daga baya." Haka SHAREEF ya amsa cup ɗin, babu musu ya sha kamar yanda tace dashi bayan yayi Bismillah a zuciyarsa After sun yi sallama ya tafi, yana kan mota ya kira Hanif ya tambaye sa inda zai same sa Ya faɗa masa, "yanzun nan ya shiga Company." "Ok I'm coming now." Daga haka ya kashe wayan ya nufi Company, kai tsaye office din Hanif ya wuce ya shiga Hanif da ya gansa yayi mamakin yanda ya ga ya sauya mishi, dalilin da yasa ya tambaye sa, "ko akwai wani abu ne?" Ɗan numfashi SHAREEF ya ja before yace, "Haseena. Haseena ta zo gidana, amma abun da ban faɗa maka ba; na sake ta tun tana can..." Tun kafin ya ƙarisa maganar farin ciki ya nuna a kan fuskar Hanif, cikin zumuɗi yace, "what kind of happiness is this? good news." Sai dai tuni ya sauya fuska sabida jin ƙarisan zancen nasa, "What! Ka mayar da ita ka ce? And you love her now?". *Happy juma'at Mubarakh fans and enjoy your weekends.😘 Love you.* [08/05, 6:04 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE33* _____"And bayan ka sake ta kuma mene ne dalilin zuwan ka gidan su yau?" Yayi maganar da tsananin mamakin jin zantukan SHAREEF Wanda shi kuma yana dafe da kansa kamar zai yi kuka yake cewa, "i don't know Hanif, and yanzu kuma ina sonta, ina son zama da ita, yanzu ta dawo rayuwata, tunanin ta a kwanakin nan ya hana Ni saƙat that's the reason da na je ganin ta, and I thought ta koma can Austria." "Hasbinallahu wani'imal wakeel!" Hanif ya furta yana tsare sa da ido ya kasa cewa komai yana faman kallonsa, yayinda yake sauraron zantukan sa da ya dage yana ta mishi bayanin halin da yake ciki da yanda yake ji a zuciya, sai da ya gama tsab before yace, "gaskiya akwai matsala, abun nan da ɗaure kai Bro, mene ne dalilin ci gaba da sonta bayan abubuwan da tayi maka a baya? Gaskiya ban yarda da ita ba, yakamata ka ɗauki mataki tun kafin abun ya zama worst irin na baya, ka dage da addu'a Bro domin samun sauƙi daga wannan bala'in da ke shirin kunno ka, bai kamata ka ci gaba da son wannan yarinyar ba sai dai akwai abun da tayi maka ne, ka san irin su ba abun da baza su iya aikata wa ba. You better ka tashi tsaye cikin addu'a ka dage i know kana da apps cikin wayanka na azkar, ka duba ko na sihiri ne da wasu addu'o'i na miyagu kayi tayi domin tseratar da kanka." Sai kuma ya girgiza kansa da ci gaba da faɗin, "wai tana son ka bi ta can ko? Kai wannan sheɗaniyar yarinya ce yakamata ka tashi tsaye ina faɗa maka Bro, don idan Iyayenmu suka ji abun bazai yi kyau ba." Ya ƙare maganar cikin baƙin ciki da damuwa Yayinda har a cikin zuciyar SHAREEF ya yarda da zancen Hanif, sai ya ji dad'i a ransa sabida samun shawaransa, don haka tun a lokacin ya soma ƙoƙarin karanta addu'a; yayinda ya fitar da wayansa yana son duba applications na azkar; ko yana nan bai goge ba Shi kuma Hanif sai ya samu damar ci gaba da zantukan sa yana ƙara ba shi shawarwari masu kyau, Daga baya ya faɗa masa, "shima yanzu ya zo zai karisa wannan ayyukan da ya rage masa, daga nan zai wuce gidansu ya ɗauki Amra tunda ya kaita wurin Momy, daga asibiti suke ya ajiye ta a can." Dalilin da yasa SHAREEF ya zauna kenan yana jiran sa tunda yace, "zai bi shi su tafi tare." Bayan ya gama aikin suka fita kowa ya hau nasa Motan, sun ɗan jima ma tunda sun yi magana da wasu daga cikin ma'aikatan nasu, Daga nan suka wuce can gidan su Daga Amra sai Momy a zaune a falon suna ɗan taɓa hira kaɗan -kaɗan suna kallo While Dady kuma sai ya basu wuri yana ɗakin sa shima yana ɗan dube-duben sa a computer Bayan sun shiga da sallama, Momy ta amsa musu ta bi su da kallo face ɗin ta da murmushi, don yanzu ba ƙaramin sha'awa suke bata ba in ta ga sun taho tare, musamman yanzu kasancewar sun yi aure sun yi nesa da su, sai suke bata sha'awa in suka shigo a tare, farin cikin ta ma daban ne, Bayan sun zauna ta amsa gaisuwar su da suka yi mata, sai take cewa, "Ina ka baro min Maryam kai baka zo da ita ba? Yakamata dai ka kawo ta mu gaisa tunda na ga alamun sai mun yi magana, tunda aka yi aure har yanzu kafarta bai shigo gidan nan ba, ai tayi haƙuri wlh da wannan ƙorafin nata, ga Hanif nan ya kawo nasa har sau biyu, kar dai a ce Matar kulle zaka zama da ita?" Dariya suka yi su dukka har SHAREEF da ba kasafai yake yi ba, Sai ya shagwaɓe fuska yana cewa, "kai Mom, wannan ƙorafi haka? But dukka-dukka yaushe muka yi auren? Ai Ni na fi Hanif hankali shiyasa ban kawo ta ba, baza ki haɗa mu tare ba." Dariya suke yi har Amra wacce ta duƙar da kanta kamar ba ta a wurin Mom tace, "eh ka fi sa hankali tabbas, na ga alama yanzu ka soma hankali." Sosai SHAREEF ya kwaɓe fuska kamar zai yi kuka yana kiran sunan ta While Hanif sai ɓaɓɓaka dariya yake yi, yace, "Momy kina so ki dawo da shagwaɓan wannan bawan Allan fa." "Eh, ai abun da nake son gani kenan don na rabu da ganin shagwaɓan sa, gwara ya koma min SHAREEF ɗina mara jin magana in ɗan ja kunnen sa; don na yi kewar wannan halin nasa." Dariya dukka suka yi, SHAREEF kuma yana shafa ƙeya har yanzu da murmushin a kan face ɗin sa, sai dai ya ƙi cewa komai ne don akwai Amra a wurin shiyasa ya ƙyale su suka yi ta tsokanarsa, Sai da abun yayi masa yawa ne ya harari Hanif yace, "ya ishe ka fa, kayi main shiru haka, in ba haka nan ba zan fasa bakin ka." Fitowar Dady da maganar sa shi ya hana su ci gaba da hiran nasu, ya sauko da ɗan jaridar sa a hannu, wayansa na gaban rigan jallabiyarsa, fuskarsa a sake yake cewa, "wai dariyan me nake ji ne ya cika min kunne? Mai ake tattaunawa ne babu Ni a ciki? To a dawo farko tunda gani na fito." Har Amra sai da ta ɗan dara sabida maganar Dadyn, Dayake tana kusa da Momy ne; dalilin da yasa ta miƙe kenan ta koma ƙasa wurin ƙafan Mijinta tayi zamanta a wurin, still kanta a ƙasa ta rufe jikinta da hijab, kwata-kwata ta kasa ɗago kanta sabida kunya da kuma rashin sabo da su, but tana sauraron zantukan nasu da suka ci gaba da yi gunun ban sha'awa da burge wa irin na iyalai masu farin ciki, Ita dai sai dai tayi murmushi babu bakin magana ko an sako ta, Dayake Momy ne ma ko Dadyn suke sako ta a zancen nasu Har Dady yana cewa, "ta saki jikinta sosai fa, nan ba a baƙunta don a yanzu ya ci a ce ta saba da su, ita ƴa ce a wurin su kar ta takura wa kanta." Duk da sun san bata magana amma sai sun ja ta a cikin zancen nasu suna raha da dariya SHAREEF ne ma daga farko bai cika yin maganar ba don ganin akwai baƙuwa a cikin su, amma kuma daga baya tuni ya ware ya manta da ita yana zuba zancen sa da shagwaɓar da ya saba yi wa Momy, don tun farko yana jin sa kamar shi ne Auta, Bare yau ya samu abun da yake so ta biye masa ba kamar baya da ta ɗauke masa wuta ba Wannan hiran ne ya ja hankulan su; basu tashi ba har sai da aka kira magriba, wani ɓangare na zuciyar SHAREEF yana can ga Maryamu; don yau ne kaɗai ya samu fita har ya daɗe haka yayi nisa da ita, tun bayan shan Angoncin sa sai yau ne ya fita ya jima haka, ya san cewa dole tana can tana kewarsa, ya so kiranta kuma bai kira ba har suka yi sallan magriba zasu tafi Bayan sun yi sallama da iyayen nasu suka ɗan musu nasiha before suka fito, Amra tuni ta shiga cikin motan Hanif, shi kuma ya tsaya da SHAREEF a wurin motan suna sake tattaunawa a kan matsalarsa, Yana sake ba shi shawaran dagewa da addu'a komai zai wuce ya manta da ita Shima dai SHAREEF ya yarda da maganganun Hanif da yake cewa, "ba haka ta bar shi ba, ta yiwu akwai abun da tayi masa." Don haka har zuciyarsa ba ya jin daɗin abun da ya aikata yau, da kuma yawan tunaninta da yake yi, zai so ya rabu da ita na har abada tunda yana da Maryamu, ita kaɗai ta ishe sa, bazai so ya juya mata baya ba, da ɗan hankalinsa yanzu a jikinsa yana ji a ransa ci gaba da son Haseena ba alheri bane, bata da wani amfani a tattare da shi A nan ma sai da suka ɗan ɓata lokaci kamar shuɗewar mintuna sha biyar, before suka rabu kowa ya hau nasa motan suka fice Har a cikin mota SHAREEF addu'a yake yi ya kama hasbinallahu wani'imal wakeel, da la'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalumin, innalillahi wa'inna ilaihi raji'un! Yana tayi a zuciya a haka har yakai gidan sa Kwana biyu kenan da saka mai gadin su a bakin gate ɗin, wani ɗan magidanci ne wanda yake musu gadin, Shi ya buɗe masa sannan ya rufe ƙofan, tun a bakin gate ɗin yayi masa gaisuwa sabida halin SHAREEF ne har yanzu bai canza ba, ɗabi'ansa ne na wulakanta mutane kowa ba kowa bane a wurin sa, kawai kayi masa aiki shine abun da ke tsakanin ku da shi, dole in ka zauna dashi a rana ɗaya sai ka gane halin sa na halin ko in kula da rashin damuwa da mutane, uwa uba wulaƙanci idan ka shiga gonansa, Don haka tun ranan farko da mai gadin ya buɗe masa gate, sai ya bi sa har wurin mota yana masa gaisuwa da kirari Nan kuwa ya haɗe fuska cikin nuna isa da gadara ya nuna masa, "ba ya son hakan, ba gaisuwa ya kawo sa yayi masa ba, aikin sa kawai zai yi, idan kuma yace zai riƙa takura masa zai kore sa a aikin ya kawo wani, bai son damuwa." Ai tun daga ranan mai gadin ya yi wa kansa karatun ta natsu, dama kwaɗayi ne da son samun gindin zama, tunda ana labarin wasu Iyayen gidan irin haka kuna girmama su sai ka ga sun ɗauke ka da muhimmanci suna ɗan maka ihisani, ashe ba haka bane a nan, don haka ya shiga taitayin sa, nan babu fuska bare ya samu na banza Shigan SHAREEF cikin gidan sai ya rufe ƙofan, sannan ya nufi hanyar ɗakin Maryamu ganin babu kowa a Falon; A nan a yashe a tsakar ɗakin ta ya hange ta, In quickly ya ƙarisa inda take yana kiran sunanta, gabansa ba ƙaramin faɗuwa yayi ba da ya ganta a hakan, hankalin sa lokaci ɗaya sai ya tashi ya ruɗe yana faman kiran sunanta da ƙarfi, yayinda tuni ya sanya hannayensa biyu ya ɗago ta and yana girgiza ta Sai dai Maryamu babu inda nata ke motsi Idan hankalin sa yayi dubu tabbas ya gama tashi a wurin, halin ruɗewan da ya shiga a time ɗin bazai iya faɗuwa ba, Amma tuni ya ɗago ta ya miƙe da saurin sa zuwa waje, ko tunanin ma ya watsa mata ruwa bai yi ba, kai tsaye motansa ya koma ya saka ta ya shiga ya danna horn tun kafin ya isa bakin gate Tuni Mai gadi ya fito daga ɗan ƙuryan ɗakin sa ya buɗe masa gate ɗin Yayinda ya fige motan ya fice ya nufi da ita asibiti, yanda yake sharara gudu nan da nan ya isa asibitin, Yana tsayar da motan ya soma ƙoƙarin fito da ita; yayinda zuciyarsa ke sake buga wa da ƙarfi tsoro ya cika sa sabida ganin halin da Maryamun take ciki, musamman da ya ji babu inda nata ke motsi jikinta yayi sanyi tamkar bata da rai a jikinta, wannan dalilin ne yasa duk ya ruɗe ya ruga da ita cikin asibitin yana faman kiran nurse's Dayake asibitin su Doctor Abbas ya kawo ta, a time ɗin ya fito kenan daga wani ward, ya hangi SHAREEF yana gudu da Maryamu a hannu, dalilin da yasa ya nufe sa kenan shima yana kiran sunan sa Da sauri SHAREEF ya juya sabida jin muryansa, sai kuma ya isa gare sa yana cewa, "doctor, help me, help..." Abun da yake furta wa kenan maganar nasa ta ƙi gaba bare baya Doctor Abbas kallon yanda Maryamun ta nanƙwaye yayi; kanta yana kallon ƙasa kamar mara rai, sai nan da nan yace masa, "ya biyo sa zuwa office." A baya ya bi sa ƙafa da ƙafa suka shiga office cikin sauri, While SHAREEF tuni ya kwantar da ita a saman gadon mara sa lafiya yana tsaye a wurin Inda Doctor Abbas ya soma ƙoƙarin duba ta yana son ya tabbatar tana da rai ko kuwa? But bai gane hakan ba, cus har lokacin babu inda nata yake motsi, duk wani wurin da ake gane mutum yana da rai ya taɓa ya ji shiru, shi kansa hankalinsa ya soma tashi; ga SHAREEF da ya tasa sa a gaba sai faman tamabayarsa yake yi yana cewa, "ya taimaka masa." Shi kansa abun ya soma basa tsoro sabida a halin da ake ciki ya soma tunanin babu rai a jikin Maryamu, don a yanda jikinta ya saki yayi sanyi ƙalau komai nata ya dena harbawa "Please Doctor, do something, kar wani abu ya same ta." Ɗago ido yayi ya dube sa jikinsa a sanyaye, sai kuma ya kasa yin magana ya ci gaba da ƙoƙarin tattaɓa ta, "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!" Abun da ya iya furta wa kenan batare da ya ɗago ya dubi SHAREEF ba Inda SHAREEF hakan ya sake saka shi a ruɗani, sosai a yanzu jikinsa ke faman rawa, haka ma muryansa da yake kiran sunan Doctor da faɗin, "what's going on? Please tell me doctor me ke faruwa?" Huci ya ja sai ya kalle sa yana faɗin, "Im so sorry..." "Noo kar ka faɗa min rubbish Malam, meke damun ta? Ka duba ta ka tsaya kana kallonta taya ya zaka san me yake damun ta?" Ya katse sa cikin tsawa a haukace cikin rikicewa; saboda kar ya ji abun da zai furta masa, wanda tuni har ƙwalla sun soma taruwa a idanuwansa sabida halin da yake ciki, lallai bazai iya yarda da cewa Maryamu ta barsa shi kaɗai ba, wannan ƙarya ne. [08/05, 6:52 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE34* _____Ganin yanda SHAREEF ya ruɗe, dole Doctor Abbas ya ci gaba da bata taimakon gaggawa sabida samun ganin tana da rai ko babu, wanda daƙyar ya iya ganowa wani jijiyarta a hannunta yana motsa wa, shima sai da yayi da gaske before ya gane sabida sai ya ɗauki some minute's yake jin jijiyar tana harbawa, Da sauri ya ce wa SHAREEF, "ina ga tana da rai, calm down please SHAREEF, go and set komai zai daidaita." Har SHAREEF ya ji sanyi a cikin ransa, amma ya kasa zama yana tsaye a wurin yana kallon yanda yake aikinsa cikin ƙware wa, Daga karshe ya kira wata nurse ta sake kawo masa wasu kayan da yake bukata har drip aka sanya mata, aka yi mata allurai a cikin ruwan Kamar shuɗewar seconni sai gani suka yi kamar zata farfaɗo, numfashin ta ya dawo amma yana sama-sama zai ɗauke tana wani irin ƙara kamar mai cutar athma Hankalinsu ya ƙara tashi abun ya cutura, iya ƙoƙarin Doctor ya rasa abun da zai yi mata, ga shi duk wani taimako sun bata amma still tana nan a yanda take; numfashin ta na ƙoƙarin fice wa har ta soma fizge-fizge zata faɗo a kan gadon, Sai lokacin ma suka kula da ƙafanta ɗaya yanda diddigen ya kumbura suntum Doctor Abbas ne ya soma kula da wurin, ya ja salati a tsorace yake nuna wa SHAREEF wurin A ruɗe SHAREEF da ya tallabo ta jikinsa yake kallon wurin, shi kansa ya tsorata fiye da tunani, ga kuma halin da ya ga ta soma yi tana fizge-fizge har wannan lokacin ba ta hayyacinta, lokaci ɗaya ta tsandara uban ihu tana son ƙwace wa a jikin SHAREEF, a wannan lokacin ya rigada yayi tunanin tabbas bazai wuce Aljanunta bane, tunda ya san tana dashi don haka ya dubi Doctor yace, "zan wuce da ita gida, bazai yiwu mu zauna a nan ba." Da sauri doctor yace, "No, ina zaka kAita kuma ban da nan? Please ka bari mu duba ta da kyau na san bazai wuce wani abun ne ya cije ta ba, tabbas hakan ne don ga alamu nan." Girgiza kansa yayi fuskarsa cike da damuwa yake cewa, "No, gwara in kaita wurin su Momy, cuz tana fama da jinnu I think su ne gaskiya, don haka take yi, ina ga bari in wuce da ita kawai." Shi kansa Doctor ya tausaya mata, don haka ba ɓata lokaci ya basa damar tafiya har wajen mota ya raka sa Mutane sai kallonsu suke yi sai dai basu san mai ke faruwa ba, amma tunda asibiti ne sun san dole majinyaciya ce; tunda a yanda suka ga an fita da ita tana ihu da bige-bige Doctor bai bar wurin ba har sai da ya ga tafiyar SHAREEF ya shiga cikin hospital ɗin, dama already ya tashi aiki zai koma gida ne kuma ya hangi SHAREEF, don haka ya je ya harhaɗa kayansa ya rufo office din sa Yayinda SHAREEF tuni ya isa gidan su, don a yanda yake tsula gudu a cikin daren nan burin sa kawai ya gansa a gida Time ɗin har ma'aikatan gidan sun kwanta, har Mai gadi ya rufe dakinsa, amma jin horn sai ya fito da sauri, dayake akwai hasken lantarki bai yi amfani da wayansa ba, sai da ya leƙa ta ƙofa ya hangi motan SHAREEF wacce ya shaida ta, don haka tuni ba ɓata lokaci ya zaro key din kwaɗo daga aljihun sa ya fito dashi ya buɗe kwaɗon da ya garƙame gate ɗin, Nan da nan ya buɗe masa jiki na rawa; don a yanda ya addabi gidan da horn ko su Momy suna jiyo wa Da gudu ya shigar da motan ya dakatar da ita a tsakiyar gidan, sannan ya buɗe murfin motan ya koma ta baya don ciro Maryamu da har yanzu tana nan cikin wannan fitan hayyacin, sai kukan ta ma da ya ƙaru tuni ta gama tuttuge gashin kanta, rigan barcin jikinta kuma tuni tayi sama ta kusa cire ta, Allah yasa akwai pant a jikinta, Don haka sai da SHAREEF ya gyara mata rigan daƙyar ya fito da ita saboda yanda take zille wa Dama su Momy da ke zaune a falo already sun ji ƙaran horn din, hakan kuma ya ɗarsa musu zargin ba lafiya ba har Dady yana tambaya, Yayinda ya rage ƙaran Tv yana ƙoƙarin miƙe wa a wurin, Daga nan ne suka soma jin kamar ihu yana ratso su Dalilin da yasa suka tashi kenan, suka nufi bakin ƙofan har da haɗawa da ɗan gudun su, Fitan su ke da wuya; suka hangi SHAREEF rungume da Maryamu a jikinsa shima ya nufo gidan, Dukkannin su sai da gabansu ya faɗi ganinsa a haka da tuni sun tabbatar da Maryamu ce a hannunsa "Lafiya SHAREEF; me ke faruwa?" Gaba ɗaya suka soma jero masa tambayoyin hankalin su a matuƙar tashe Yayinda SHAREEF ya soma ƙoƙarin kora musu bayani a ɗan ƙanƙanin lokaci Tuni Dady yace masa, "ya mayar da ita mota su wuce da ita wurin Malam." Don a lokacin sun fahimci cewar ciwon ta ne ya tashi, Nan Dady ya koma ya sako takalmansa yana cewa Momy, "ta jira su; su je su dawo." But Momy tace, "a'a su tafi tare kawai." Don haka gaba ɗaya suka koma cikin motan SHAREEF, Momy ta riƙe Maryamu a bayan mota, su kuma suka shiga gaba suka bar gidan, Tun a hanya Dady ya nemi wayan Malamin da yake duba ta yayi masa kira, Sai a kira na uku sannan ya same sa, Nan ya zayyane masa halin da ake ci ya faɗa masa, "suna nan tafe a hanya yanzu." Malam yace, "to shikenan yana jiran su sai sun zo." Dukkansu babu natsuwa a tattare da su, musamman Oga SHAREEF wanda tuni ya daɗe da rasa natsuwarsa ga tashin hankali, Dady yake masa kwatancen gidan har suka isa kofar gidan Malamin Already har ya fito yana jiran su a waje, Don haka shi ya jagorance su zuwa ciki, Inda SHAREEF ya ɗauko Maryamu daƙyar ya shiga da ita ciki A gabansu Malamin yasa aka kwantar da Maryamu a saman tabarma, sannan ya fara gabatar mata da karatun Alkur'ani bayan ya riƙe ta sosai Da farko kukan kawai take yi mai tayar da hankali, amma daga karshe sai ta koma ihu ta ci gaba da fizge-fizge tana shirin kamar zata tashi Nan Malamin ya sanya SHAREEF ya zo ya riƙe ta gam, dayake yanzu babu tsoron don ta lafiyar Matarsa yake yi, nan kuwa ya zo ya rungume ta ya manna kanta a ƙirji ya haɗa da hannayenta yayi mata mugun riƙo irin nasu na Maza, gaba ɗaya ƙarfin sa ya samu ya danna mata amma duk da haka ya gaza riƙe ta, don abun yayi worst da yawa, Sai da Dady ya taimaka tare da Malamin ya ci gaba da zuba mata karatu Dama can tun farko bata taɓa magana ba duk karatun da za a yi mata ba sa magana sai dai tayi ta ihu, amma abun mamakin yanzu sai ta fara maganganu tana faɗin, "su sake ta ba ta son karatun, kar su kashe ta su taimaka mata." Nan fa Malamin ya ƙara ƙoƙarta wa wajen ci gaba da karatun da ƙarfinsa yana yi yana karanto ayatul kursiyyu, sai da ya galabaitar da ita sosai before ya dakata ya fara tambayarsu dalilin shigan su jikinta? Tana haki idanunta suna zubar da ruwan hawaye kamar ana kwarara mata ruwa, gaba ɗaya ta jiƙe da zufa idanunta sun kaɗa sun yi jazur sun sake manya har wani nama-nama suke yi na ja, Da farko ta ƙi magana sai da ta ji yana ce mata, "zai ci gaba da karatun." Sannan daƙyar ta buɗe baki ta soma magana da muryan Maza, maganar nata na fita ɗaiɗai tana kuka sosai take cewa, "bazan yarda ba wannan karon, tunda suka illata ni da abun da na fi ƙauna, sun so kashe ta a lokacin da nake jikinta, sun yi min illa ba kaɗan ba, bazan taɓa yarda ba sai na ɗauki fansa; domin baza a taɓa min ita in ƙyale ba, duk wanda ya so cutar da ita sai mun ɗauki mataki." "Kai meye haɗin ka da ita har ka shiga jikinta? Ban muku iyaka ba ashe har yanzu kana jikinta?" "Ni bazan iya barin ta ba, babu wanda ya isa ya hana Ni taraiya da ita, domin ita Matata ce, na aure ta bazan sake ta ba, ina sonta ina ƙaunarta tun tana ƙaramarta, don haka bazan iya barin ta ba, domin idan aka ce za a raba mu komai zan iya yi." Sai ta ja numfashi tana ci gaba da haki numfashin ta na ɗauke wa kamar zata shiɗe, tana ɗaga ƙafanta ɗaya da diddigen ya kumbura Girgiza kansa yayi yana jinjina ƙarfin halin sa, sai kuma yace, "yanzu faɗa min waye yake son cutar da ita? Ko akwai wasu ne bayan kai a jikinta?" "A'a babu wasu, domin kowa ya san Ni ne Mijinta bazan taɓa barin wani ya shige ta ba, kuma bazan taɓa bari a cutar da ita ba, shima Mijinta don na ga tana matuƙar ƙaunarsa ne shiyasa na bar shi, domin na so cutar dashi amma na gagara ganin halin da take shiga a kansa, amma kuma sabida yanzu za a kashe min ita, kun shammace ni kun yi mata aure batare da sani na ba, amma idan wani abu ya faru da ita daga shi har wacce take son kashe min ita don shi; sai na kashe su bazan bar su ba, a taimaka a cire min wannan ƙarin da ke ƙafana, ana cutar dani da ita, idan ba a cire ba zata iya rasa ranta." Shi Malam ma sai lokacin ya kula da ƙafan, haka suma su Momy, amma hankalin su yayi matuƙar tashi duba da abin da Aljanin ke faɗa, to mai hakan ke nufi? Waye yake son cutar da ita saboda SHAREEF ɗin su? Shi kansa SHAREEF duk ya ɗimauce don jin abun da ke faruwa, har jikinsa ya ɗauki rawa sabida tashin hankali da tunanin waye ya aikata hakan duk sabida shi? While Malam tuni ya ɗago ƙafan yana kallo, sai kuma yace, "wannan ciwon mene ne? Zamu so mu san ciwon mene ne sabida mu san mai za a yi mata? Ka faɗa mana abun da ka sani akai da wacce take son cutar da ita in har ba kai ka aikata mata hakan ba?" Kuka ta fashe dashi, sai tace, "don Allah ku taimaka ku cire mana muna azabtuwa, ƙarin Kunama ne da cizo, an yi ne don kashe ta amma nayi ƙoƙarin ceton ta wanda aka ɗana min a madadin ta, nayi alƙawari idan ku ka cire min zan faɗa muku wace ce domin tana da hatsarin gaske." Jin hakan yasa Malam ya koma duba ƙafan yana kallo, gaba ɗaya ta kumbura tayi suntum har yatsun sun shige sun zama kamar babu yatsu, Sosai abun ke basu tsoro sabida ganin yanda ƙafar take hauhawa kamar flower, Dole Malam yace, "sai an yi mata alluran ƙarin cire Kunama kuma an bata magunguna, don haka a hanzarta a kira Likita." Dole SHAREEF ya ɗauki wayansa yayi kiran Doctor Abbas, don shi kaɗai ne zai iya taimaka musu yanzu ya nemo musu maganin sai yayi mata alluran, Don haka ya kira sa a waya yayi masa bayani tare da kwatancen inda zai same su Shi kuma Malam ya ci gaba da tofa wa wurin addu'a duk wani taimako ya yi ƙoƙarin bata, har an ɗaure ƙafan sabida yana yin gaba yana hawan mata can saman ƙafa Doctor Abbas da ya iso shi yayi mata alluran har guda uku, a nan take, Sannan aka bata wasu magungunan ta sha Daga nan kuma sai ta soma barci bata sake sanin inda kanta yake ba Tabbas sun shiga damuwa kuma sun tausaya mata, Bayan ganin haka sai Malam yayi musu bayani da cewa, "akwai abun da ke son cutar da ita ne amma Allah ya tsare, don haka gaskiya dole kuyi taka-tsan-tsan a kula da ita wurin taimakon ta da addu'o'i, don irin hakan zai iya bada damar da ciwon ta zai dawo sabo ya riƙa tashin mata sabida halin da ta shiga, kuma idan hakan ta kasance zata sha wahala ne, kun ji abun da Aljanin ya faɗa duk yanda aka yi akwai wacce take son cutar da ita, dole a ɗauki mataki idan ba haka ba abun zai yi muni, Allah ya tsare gaba a kula da ita sosai, akwai addu'o'in da zan bata ta riƙa ƙoƙarin yi sannan da wanda za a shafa mata a wurin, insha Allahu zai saɓe sai a haɗa mata dana asibitin har Allah yasa ta samu lafiya." Doctor Abbas shi dayake yayi musu sallama ya tafi, su kaɗai suka rage a wurin Malam na kora musu bayani, sannan ya haɗa musu da magungunan ya sallame su Dady yayi ta mishi godiya, daga ƙarshe ya ba shi ladan aiki tare da wanda za a yi wa almajirai sadaka a ci gaba da taya su addu'a SHAREEF shi ya ɗauke ta ya mayar da ita cikin mota, sannan suka tafi zuwa gidan su, Tunda can Dady yace, "ya wuce da su kawai sabida a kula da ita." Ƙarshe dai shima SHAREEF a can ya kwana, Dayake tun a daren suka yi waya da Hanif ya zayyane masa komai, don ya kasa hakura ya bari sai da safe, abun ya tsaya mishi a rai sabida tunanin wanda yake son cutar mishi da Mata, shi dai bai san wa zai zarga ba Amma tashin farko Hanif sai yayi tunanin ko dai Haseena ce, don zuciyarsa ita take zargi, don haka yace masa, "wlh Ni ina kyautata zaton Haseena ce zata yi maka haka, duk wani zargi ya nuna ita ce, ita ce take son cutar da ita sabida soyayyar da take maka, duk da zato zunubi ne amma babu mahalukin da zai maka haka sai ita, bare dama mun fara zargin koda sihiri a tattare da ita da take maka; sai ga shi abu ya fito fili." Shi kansa SHAREEF ya amince matuƙa da zancen Hanif, sai yanzu tunanin sa ya basa haka, amma in ko haka ne tabbas zai ɗauki mummunar mataki a kanta, bai ma taɓa tunanin haka take ba sai yanzu da take ƙoƙarin bin sa da sharri, lallai dole su san abun yi Dayake dare ya tsala sosai, dole suka yi sallama basu gama tattaunawa ba, yayinda Hanif yace masa, "zai shigo da safe sai su san abun yi." Shi kuma SHAREEF kasa haƙura yayi ya nemo numban Haseena wanda yasa a Blacklist, sai ya cire ya kira ta Ring ɗaya sai kuwa ta ɗauka tunda tana a farke ba barci take yi ba, suna abun da suka saba, a tunanin ta shirin su ne yasa ya kasa haƙura sai da ya kira ta, don haka cikin yanga da kisisina tace, "dear, kai ne a daren nan? Kamar ka san ina kewarka na gaza sukuni ina jiran amsar ka." Takaici da baƙin cikin maganganun ta yasa shi daka mata wani irin tsawa yace, "rufe min baki muna-fuka, ashe dama haka kike mai bak'ar zuciya mara imani da tausayi? Ban san yaushe kika sauya ba Haseena amma ba haka kike ba, asirin ki ya kusan tonuwa sabida tunanin cewa dole sai kin mallake Ni, haba abun da mamaki a yanda na kasa natsuwa zuciyata take son min yawo da hankali duk a kanki, ashe da dalili tunda ba ki bar Ni haka ba, but ki ji duk abubuwan da kike shirya wa a kaina kike son cutar min da Mata, kin yi ƙoƙarin ki kashe ta sabida ina tare da ita don mummunar nufin ki a kaina." Cikin fushi da ɗaga murya ya ƙara da cewa, "idan har kika kuskura kika cutar min da Maryama, na rantse da Allah sai na wulaƙanta miki rayuwa, kuma duk abun da kike shirin aikata wa ki ci gaba da aikata wa bazan taɓa ƙyale ki ba duk ranan da dubun ki ta cika." Sai ya ja tsaki ya kashe wayan yana wurgi dashi, Yayinda ya kasa zaune ya kasa tsaye yana tunanin matakin da zai dauka, lallai duniya abun tsoro ne, dole ya san yanda zai yi ya ceci kansa daga sharrin ta, don idan ta gusar masa da hankali komai zai iya aikata wa bai sani ba, tunda a yanda yake jin ƙaunarta ɗazu zuwa yanzu kuma ya ga bambanci, dole ne akwai wani abu, addu'a shi ne takobin sa domin tsira da mutuncinsa; musamman a kan mummunar ƙudirin ta a kansa, Don haka bai ga ta zama ba sai ya tashi ya shiga toilet ya ɗauro alwala, abun da tunda yake bai taɓa cewa ga ranan da ya tashi sallan dare ba, Ibadan da bata dame shi ba sai yanzu da ya soma dawowa hayyacinsa, ya san cewa shi ne takobin sa, duk wanda ya tsaya ga Allah ɗaya tak ya koma gare sa da ibadu, babu wani mahaluki da ya isa ya cutar dashi, kuma babu abun da zai nema ya rasa in har ya miƙa buƙatar sa ga Allah, a wurin sa kaɗai zai nemi taimako a kan wannan mummunar yanayin da bai san ta inda za a farmake sa ba. 🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆🔆 Yayinda a wannan daren Haseena ta shiga tashin hankali tsantsa sabida jin furucin SHAREEF, abun da ɗaure kai, ko in ce sun sha mamakin yanda aka yi ya gane Haseena nan take, har kuma da maganar kokarin kashe masa Mata, to taya ya kenan hakan ta faru? Daga ita har Nana tambayar da ya shige musu duhu kenan, Kuma hakan na nuni da cewan har yanzu tana raye bata mutu ba, don haka ko a nan dole akwai babban al'amarin da ya wakana har take raye bata mutu ba Take a nan suka yi amfani da ƙarfin tsafin su suka bincika komai, duk da basu san ya aka yi ba amma sun gane Maryamu tana raye Hankalin Haseena idan yayi dubu to ya tashi, yayinda ta ɗauki alwashin wlh in har bata samu SHAREEF ba, to babu wata Mace da zata same shi, in har bata ci galaba a kansa ba sai dai ta sadaukarwa da Ƙungiyarsu shi, daga shi har Matar tasa da ta kasa kashe ta, Kamar yanda ta ɗauki alwashi tun farko to sai ta aikata, sai dai su mutu dukka amma kishi bazai barta tana gani SHAREEF ya zauna da wata bayan ita ba, ko mene ne sai tayi don ƙwato shi. [09/05, 6:53 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE35* _____Da sassafe sai ga Hanif ya zo gidan shima, lokacin su Momy ya samu a kan dainng suna karyawa, Ya wuce wurin su ya gaishe su; bayan ya zauna a kan ɗaya daga cikin kujerun Dinnig ɗin Suka amsa a tare dukkansu, tare da tambayarsa Iyalinsa? Yace, "Alhamdulillah tana gaishe ku." "Muna amsa wa, ya batun maganar neman lafiyarta? Ana samun ci gaba ko har yanzu shiru ne?" A cewar Dady da ya ajiye Cup din hannunsa yana mai kallonsa Hanif yace, "Dad, to Alhamdulillah zamu ce, but har yanzu dai shiru ne amma tana kan shan magani ne, kuma muna koma wa asibitin kamar yanda suka ce mu riƙa yi, ana dai ta treating ne sai dai mu ga abun da hali zai yi a nan gaba." Daga shi har Momy suka haɗa baki wajen faɗin, "Allah ya bata lafiya, yasa a dace." Ya amsa sannan ya tambayi jikin Maryamun yana faɗa musu, "Bro ya kira sa ya faɗa mishi komai." Momy tace, "jiki da sauki, but har yanzu bata farka ba dai, SHAREEF ɗin ma yana ɗakin ka shiga ka duba ta, tana nan a ɗakin ta." "Ok bari in je." Ya miƙe yabar wurin zuwa ɗakin kwanan Maryamu a da, Da ya shiga ya samu SHAREEF zaune a bakin gadon Shima jin sallaman sa ne sai ya motsa daga kallon Maryamun da yake yi, sannan ya gyara mata blanket ɗin da aka rufa mata jikinta dashi, ya rufe mata ƙirjinta da ke buɗe; tunda har yanzu rigan barci ne a jikinta Tahowa Hanif yayi ya zauna a bakin gadon shima, sannan ya kalli SHAREEF yace, "ya jikin nata?" "there is no easy, but please bless us with prayer, she still hasn't woken up, she still hasn't moved, and ji be yadda ƙafarta ta koma." Ya yaye mishi blanket ɗin yana buɗe masa ƙafarta Ba ƙaramar tsorata Hanif yayi ba, wani irin mugun tausayinta ya kama sa har tsigan jikinsa yana tashi da ganin yanayin ƙafar, don ma wai ba tun jiya ya gani ba tunda yau da sauƙi za a iya cewa; ya saɓe sosai ba kamar da ba, Yayinda ya ɗauke idanunsa da sauri yana duban SHAREEF ɗin, shi kansa yanda ya ga SHAREEF ya sauya mishi a ɗan wannan lokacin ya tabbatar yana cikin damuwa, tunda ga shi nan fuskarsa ta nuna, har ya zurma tunda ko abinci bai ci ba daga daren jiya zuwa yau, Kuma su Momy sunyi-sunyi ya taso ya karya ya ƙiya, "I'm so sorry Bro, insha Allahu Allah zai bata lafiya, sai dai wannan maganar ba na jin zamu barta a tsakaninmu, yakamata mu sanar da su Momy su san cewa ga abun da muke tunani, tunda zahiri ya nuna dole akwai maƙarƙashiya a cikin wannan abun, kuma ba wanda zai yi mata haka sai Haseena, Haseena ce masoyiyarka, a yanda ku ka so juna komai zata iya yi domin kai, yanzu hankalinka ba ya kanta; dole zata nemi ta dawo da kai gare ta." "Yes i know..." Sai kuma yayi shiru ya kasa ƙarisa maganar yana mai ɗaura hannunsa a saman goshin Maryamu, A haka kamar zata yi magana, sai dai har yanzu ba ta motsawa sai numfashi da take sauke wa kaɗan-kaɗan, Wani irin ɗaci yake ji a zuciyarsa, ji yake yi tamkar ya dawo da ciwon da ke jikinta jikinsa, bai taɓa tunanin akwai lokacin da zai damu da damuwar baiwar Allan nan ba, sai ga shi komai ya sauya, ta shiga zuciyarsa, yana mata soyayya; soyayyar da bai taɓa yin ma wata ƴa mace a duniyar nan ba, yanda yake jinta a zuciya yana jin zai iya sadaukar mata da komai da kowa nasa in har zata yi farin ciki; har ransa yana jin zai iya sadaukar mata domin ya ga ta kasance cikin farin ciki, a duk second ɗaya da wucewar minti ƙaunarta da tsananin tausayinta ne yake ratsa mishi zuciya, shiyasa farin cikin sa gaba ɗaya ya ƙaurace mishi, ba ya jin daɗi in ba ya ga ta samu lafiya ba, duk inda magani yake in har zai sama mata lafiya zai iya zuwa ya nemo mata, idanunsa sun kaɗa sun yi jazur sun ƙara ƙanƙance wa sabida kukan da yayi jiya; da kuma rashin barci da bai samu ba, uwa uba tashin hankalin da yake ciki, "Wlh in har wani abu ya samu Maryama; bazan taɓa ƙyale Haseena ba, tabbas zata yi dana-sanin sanina a cikin rayuwarta, domin Maryama ita ce farin cikina a yanzu, ita ce jin daɗina da komai nawa a duniya, ina matuƙar son Maryama! kuma zan so ta har numfashina ya ɗauke, zan bauta mata a dukkan rayuwata!" Ya ƙare maganar hawaye suna ɗiga a kan kuncinsa, yayinda suke sauka saman nata fuskar kasancewar yayo kusanci da ita sosai; still hannunsa na a saman goshinta yana shafa har saman dunƙulallen gashin kanta da ke narke kamar kan Maza Hanif kuwa shiru yayi yana kallonsa yayinda yake jin sanyi a cikin zuciyarsa, tabbas ranan da yake jira ne ta zo, ranan da zai ga SHAREEF ya so Maryamu ya tausaya wa rayuwarta, sai ga shi yana ganin tsagwaron soyayyarta a cikin idanunsa, wanda bai taɓa tunanin son nata har yakai hakan a zuciyarsa ba, Hannu yasa ya dafa masa kafaɗa before yace, "zata samu lafiya da yardan Allah, ka zama mai ƙwarin gwiwa My Brother, zan je in sanar da su Dady abun da ke faruwa, don bazai yiwu mu ɓoye musu ba, and ka zo mu je tare please." Kamar zai ce mishi a'a, sai kuma ya ɗauke hannunsa daga jikinta yana mai share hawayensa, ya miƙe ya bi bayansa suka fita A hankali ta soma motsa ayes ɗinta tana ware yatsun ƙafarta, idanunta a rufe suke sai dai tun lokacin da SHAREEF ya soma magana ta farka, kasa motsi tayi sai da suka bar ɗakin before a hankali ta fara moving tana mai ware manya-manyan idanunta da suka canza kala gaba ɗaya, suka yi wani irin luhu-luhu suka ƙara fitowa kamar zasu faɗo, Take ta mayar da idanuwanta ta rufe sabida yanda take jin jikinta tamkar ba nata ba, babu wani sauran farin ciki a tattare da ita sabida duk yanayin ya sauya mata, kanta ma ta kasa ɗagowa bare ta motsa ƙafafunta, musamman mai ciwon da take jin kamar ba a jikinta yake ba, zugi yake mata tun daga can cikin namanta wani irin azaba na ratsa ta, ga kanta kamar zai ɗaɗɗage, Daƙyar ta iya ɗago hannunta ɗaya tana kama goshinta ta ƙanƙame bakinta tana juya kan, nan da nan wasu zafafan hawaye suka soma gudun tsere a kan kumatunta, da ta kasa jure wa kuma sai ta fashe da kuka babu mai jinta a lokacin; domin muryanta tayi ƙasa ta dishe sosai ba ta iya yin kukan da ƙarfi sabida azaban ciwon kai. *** Su Momy sun sha mamakin abun da Hanif ya gama sanar musu, Ita Momy dayake tana da saurin hawa nan da nan ranta ya ɓaci kuma hankalin ta ya sake tashi ainun, nan take cewa, "tabbas idan haka ne dole mu ɗauki mummunar mataki a kan yarinyar nan, don baza ta zo ta shiga rayuwarmu sannan tace zata muzguna mana ba, mai Maryam tayi mata da zata cutar da ita? Idan ta kashe ta ita don Ubanta zama zata yi tayi gadin duniyar? Ai kuwa komai zata yi in har ina numfashi baza ta sake zama da igiyar auren ɗana ba, in har Ni na haife shi kuma ina numfashi wlh sai na nuna mata bata isa ba tayi kaɗan ko me zata yi." Dady yace, "ya isa Deeja, wannan maganar fa zargi ne ba a tabbatar ba, sannan zato zunubi koda ya kasance gaskiya, babu ta yanda za a yi mu zarge ta bayan bamu da masaniyar cewa ita ce tayi hakan ko ba ita ba?" Momy tace, "wanne tabbatar wa ya rage kuma Alhaji? Kana dai jin abun da wannan Aljanin ya faɗa, cutar da ita aka yi a kan SHAREEF, sannan ita Haseenan ita ce wacce ya aura, sannan ga ƙudirin da take shirin aikata wa a kansa, ba don Allah ya tsare da addu'ar da yake yi ba ai da tuni ta ci galaba a kansa, tunda ai yanzu ya rabu da ita meyasa ya ci gaba da jin soyayyarta? Sannan maiyasa ta dawo rayuwarsa? Da yanzu wani zancen ake yi tunda muna ji muna gani zai bi ta wata ƙasar idan ta gusar mishi da hankali, yanzu in bamu san hakan ba sai dai muyi fushi dashi daga ƙarshe ta raba shi da kowa nasa." Jinjina kai Dady yayi yace, "haka ne, amma duk da haka mu bamu da hujjar ɗaukar mataki a kanta, Allah Ubangiji ya mayar mata da abun da tayi mana in har tana da hannu a ciki, mu namu addu'a ne musamman kai SHAREEF, yana da kyau ka sake dagewa da ibada da addu'a domin shi ne takobin kowanne mumini, muma zamu taya ka da shi insha Allahu, sannan a kan Maryam kuma insha Allahu zamu sake tashi tsaye a kanta wurin samun lafiyarta, Allah zai shige mana gaba kuma mun yarda shi ne mai yi ba wani Mutum ba, don haka mu saka a ranmu babu wanda ya isa ya cutar damu in har ba Allah ne ya ƙaddara hakan a kanmu ba, mu bar maganar nan a tsakaninmu mu fauwala wa Allah komai, Allah ya bata lafiya." Dukkansu suka amsa da Amin While Momy da ta ga SHAREEF yana shirin tashi, sai tace mishi, "ya koma ya zauna ya karya." Cike da damuwa yace, "Mom, bazan iya cin komai ba har sai na ga Maryama ta farka, zan je in duba ta." "No koma ka zauna My son, idan baka ci abinci ba kaima so kake yi ka rafke mana? Ji be har ka zurma duk ka mutsutstsuke, addu'a zaka riƙa yi ba wai saka damuwa a ranka ba, ka koma ka zauna ka ci abinci sai ka je ka duba ta." A cewar Dady kenan yana kallon sa Dole SHAREEF ya zauna tunda ba shi da yanda zai yi, amma ya san bazai iya cin komai ba Hanif ne yace, "bari in haɗa maka da kaina Bro." Momy kuma sai ta miƙe, "Ni bari in je wurin ta in zauna da ita, tunda farkawar ta muke so a soma bata magungunan ta." Daga haka tabar wurin zuwa ɗakin da Maryamu ke ciki, A lokacin da ta shiga ta tarar da ita tana ta kuka tana riƙe da kanta sai nishi take yi, Da saurinta ta ƙarisa gare ta hankalin ta a tashe tana kiran sunanta, yayinda ta kama hannunta da ke saman kan nata ta sauke tana mai ƙoƙarin tallabo ta tana jero mata tambayoyi "Kaina Momy, zai cire, ki yi min addu'a zai cire, don Allah ki taimaka min zan mutu." Haka take faɗa tana kuka ta kasa buɗe idanunta ma saboda azaba Momy kamar tayi mata kuka haka take ji, ba ƙaramin tausayi ta bata ba, da sauri ta kama mata kan ta soma koro mata addu'o'i a fili tana tofa mata A hankali kuma sai ta soma jin azaban yana rage wa, tun tana kukan da iya ƙarfin ta har ta soma ragewa tana ƙara ƙanƙame Momyn Sosai Momy tayi mata addu'a tana ta tofa mata har sai da ta tambaye ta, "shin ya dena mata ciwon?" Daƙyar ta gyaɗa kanta a hankali tana buɗe idanun nata, sai dai zugin da ƙafarta ke faman yi yasa tace, "Momy saura ƙafana, tana min ciwo sosai kamar zata cire, shima ki yi min addu'a na kasa ɗaga wa." "To ki dena kukan haka nan, kinga shi ke ja miki ciwon kan, bari in yi miki insha Allahu za ki ji sauƙi." Sai ta koma wurin setting ƙafan; tare da ɗago ta zuwa jikinta ta ajiye a hankali gudun kar ta ji zafi, nan ma addu'ar ta soma mata tana ta tofa mata A haka SHAREEF ya shigo ɗakin ya tarar da su a haka, da sauri ya isa wurin nasu yana mai farin cikin ganin Maryamun ta farka, zama yayi saman bed side drowa yana mai riƙo hannun Maryamu A nan take ta buɗe idanunta, yayinda ta zuba masa su sun cika fam da hawaye sun kaɗa sun yi jazur sun kumbure Da sauri ya washe baki yana mai shafa face ɗin ta, while yace, "Maryama, kin farka? Ya jikin naki?" Shiru tayi don baza ta iya magana ba a halin da take ciki na ciwo, sai dai ta kafa mishi ido tana kallonsa tuni hawayen idanuwanta sun ci gaba da zuba Momy tace, "SHAREEF, yanzu ɗauko maganin ta a fara bata tunda ta farka, ga su can ka kwaso su sai ka bata, Ni bari in ci gaba da tofa mata addu'ar a ƙafar; tace yana mata zugi." "To Mom." Ya amsa yana tashi ya nufi inda aka zuba magungunan saman dressing mirror, Shi ya kwaso da kansa ya soma bata after ya fita ya samo ruwa tunda wani kwaɓa wa za a yi akwai na ƙafa da ake shafa mata Tare suka dawo da su Dady suma suka shigo cikin ɗakin, sun ji daɗin yanda Maryamun ta farka, musamman bayan da aka soma bata maganin a hankali ta soma washe wa natsuwarta yana dawowa jikinta, Ba ƙaramin farin ciki suka yi ba sun zauna gaba ɗaya a tare da ita suna ta mata sannu After an gama bata maganin, Momy sai ta hana a shafa mata na ƙafan, tace, "SHAREEF ya je ya ɗauko mata kayanta a gida ko kala biyar ne, zata yi mata wanka yanzu inyaso sai a shafa mata maganin." Don haka suka fita gaba ɗaya suka bar Momyn da Maryamu, While SHAREEF tare da Hanif suka fita a tare zuwa gidansa zai raka sa Ko kafin su dawo Momy ta taimaka mata tayi wanka har ta shafa mata mai tunda garin akwai hunturu, yanayin sanyi ya fara shiga, da kanta ta amshi kayan ta saka mata sannan ta shafe mata ƙafar da maganin, Shi kuma SHAREEF ya je ya haɗo mata break first Momy ta amsa ta bata da kanta Haka suka mayar da ita kamar ƙwai a gidan nan, ko jirgawa SHAREEF ba ya yi a kusanta yana manne da ita don a jikinsa ma take kwance, yayi ta rarrashinta yana gaya mata kalamai masu sanyi da daɗi a cikin kunnenta, duk don ya faranta mata Har Hanif bai bar gidan ba suna tare har dare sannan ya tafi While SHAREEF kuma a gidan ya sake kwana Sai dai kuma sabon al'amarin da ya sake kunno wa zuwa safe, kamar wasa jikin Maryamu yayi sauƙi har an fito da ita Falo tunda ba ta iya tafiya, ƙafarta ta kumbura suntum ta ja ruwa sosai, SHAREEF ke zaune kusa da ita yana bata tea a baki, Kawai sai ta soma aman jini lokaci guda ta sarƙe da tari numfashinta ya soma sama da ƙasa, nan da nan jini ya jiƙa gaban riganta yana fita ta hanci da baki Tsananin ruɗe wa da tashin hankali ya riske su, da gudu su Momy suka ƙariso wurin sabida jin kiran da SHAREEF yake musu ya gama ruɗe wa yana kiran sunan Maryamu da ta dena motsi idanunta sun koma fari kamar babu rai a jikinta, Take ya fashe da kuka yana salati yana cewa, "Momy ta mutu, ta mutu Momy, ku taimaka min don Allah." Ya rungume ta ƙaƙam yana girgiza ta yana kuka. [11/05, 9:20 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE36* _____Bazan iya misalta muku halin da suka shiga ba a sakamakon ganin yanda Maryamu take fitar da irin wannan jinin, babu numfashi a jikinta, Musamman SHAREEF wanda kuka kashirɓan yake yi yana ta kiran sunan ta kamar wanda ya zauce shima, domin a lokacin ya sadakar ta mutu Ita kanta Momy hawayen take zubar wa domin ta kasa jure wa Dady ne mai ƙarfin hali har ya iya ɗaukar Maryamun tunda SHAREEF ya kasa, yace, "su wuce asibiti." Shi ya saka ta a mota sannan ya kira driver yace, "ya tuƙa su zuwa asibiti." A halin da suke ciki a rikice suke babu mai iya tuƙa motan Gaba ɗaya suka wuce zuwa asibitin, Dady sai rarrashin SHAREEF yake yi ganin yanda yake ta kukan ya kasa yin shiru, Yace, "kuyi haƙuri ku dena wannan kukan, ba shi ne maslaha ba, addu'a zamu yi mata, Allah ya tashi kafaɗunta." Amma sam SHAREEF ba ya iya jinsa, shi ya riƙe Maryamun a jikinsa sai tattaɓa mata face yake yi, in yayi-yayi kuma sai ya koma ya rungume ta ya sake fashe wa da wani sabon kukan A haka har suka ƙarisa hospital, yayinda tuni SHAREEF ya fitar da ita ya nufi asibitin da gudun sa, Su Dady suka bi bayansa zuwa ciki, Wurin Likitan Dadyn suka nufa tunda asibitin ne aka kawo ta Dayake sun tarar dashi nan da nan ya sanya aka amshe ta aka shigar da ita emergency, ƙarshe oxygen aka sanya mata sabida ganin bata numfashi, daga nan suka fara bata taimakon gaggawa, Likitoci biyu ne a kanta sai wasu Nurse's su uku Yayinda su SHAREEF suna haraban wurin hankalin su a mugun tashe, suna ganin yanda ake shige da fice daga cikin ɗakin, SHAREEF ya kasa tsayuwa ma illa zama da yayi a ƙasa a jikin bango ya takure kansa, a lokacin ya dena kukan amma idanunsa sun ƙanƙance sun yi jazur da su, ko gani sosai ba ya yi sabida yanda suka tara ruwan hawaye, zuciyarsa kamar zata fashe don baƙin ciki, ba ya son ya rasa Maryamu a wannan lokacin, domin a yanda yake matuƙar ƙaunarta ji yake yi sai dai ya bi ta can, saboda bazai iya rayuwa babu ita ba, ya saba da ita a ɗan ƙanƙanin lokacin nan, fatansa kawai Allah ya tashi kafaɗunta yasa baza ta mutu ba, sai ga hawaye shaa sun ci gaba da zuban masa, sai yayi saurin ɗaura kansa a ƙafafunsa yana sakin numfashi mai wahala jijiyoyin wuyansa dana kansa duk sun fito masa raɗo-raɗo, fuskar nan ta sake ja tayi kamar ɗanye Ƙarshe suma su Momy wuri suka samu suka zauna sabida sun kasa tsayuwa, A inda Momy take ba shi baki cike da tausayinsa, tana gaya masa, "ya riƙa addu'a, yanzu addu'a Maryam take bukata, babu abinda zai same ta insha Allahu." Itama tana yi tana share hawayen face ɗin ta sabida tsananin tausayin Maryamun Ba a jima ba a lokacin Likitan ya fito hankalin sa a tashe sabida sun kasa shawo kan matsalar, basu gane komai ba, har yanzu ba ta motsi sai dai sun tabbatar akwai rai a jikinta, sun yi iya yin su basu gano komai ba, infarct ma jinin da ke ɗiga ta hancinta da bakinta still zuba yake yi, sun rasa yanda zasu yi su tsayar, ya fito a tsorace hankali a tashe ya nufi wurin su Suma tuni sun miƙe tunda suka hange shi, Dady yayi saurin tambayarsa shima hankalin nasa a matukar tashe kamar zai yi kuka? "Be patient, it's too bad, we don't know what's wrong with her, abun tashin hankalin her blood refused to stop, we can't stop it, we don't know what's wrong with her, we need more information to save her life before we lose her Well, I'm not sure she'll be alive for more minutes." "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un..! Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un..." Abinda suke furta wa kenan sun gaza yin magana suna sauraron Likitan da ke ƙara musu bayani Yayinda SHAREEF ya gaza motsi ma sabida halin da yake ciki, tamkar ƙirjinsa zai fashe don ɗaci da zafin zuciya gami da tashin hankali Before suyi magana sai wata nurse ta rugo aguje tana kiran sunan Likitan, tana faɗa masa, "yarinyar tana motsi yanzu haka, tana can tana bige-bige sun kasa riƙe ta." Da jin haka sai likitan ya bi bayanta da saurin sa, While SHAREEF ma ya take masa baya don bazai iya jira a nan ba, dole ya je ya ga halin da take ciki, Hakan yasa suma su Dady suka bi bayansa a rikice Koda suka shiga suka tarar da Maryamu a kwance a ƙasa ta rikito, sauran Nurse's din sun yi ƙoƙarin kama ta amma sun gaza sabida yadda take fizga tana wani irin ƙara kamar wata mai farfaɗiya, idan tayi miƙa ɗaya sai dukkansu sun kasa dawo da ita dai-dai sun kasa nanƙwaya ta, tana son miƙe wa amma ta gaza sabida ƙafanta, sai wani irin ihu take yi mai firgitar da mutane Tunda suka ga haka sai Dady ya ɗauki waya da sauri jiki na rawa ya kira Malamin da ke duba ta, ya ba shi information na abun da ke faruwa tare da faɗa masa asibitin da suke a yanzu haka, Bayan ya gama wayan sai ya nufi inda suke ana ƙoƙarin ɗaura Maryamun a kan gadon amma sun gaza, har da SHAREEF shi ya riƙe ta gam ya ƙi sakinta, Dady yace, "please doctor a samu a yi mata taimakon gaggawa before Malamin da ke duba ta ya zo, ina tunanin ciwonta ne na aljanu suka tashi don dama tana da matsalar, idan ya zo sai yayi mata koda addu'a ne." Jin hakan sai Likitan ya haɗa wani allura da ke sa barci, ya zo dai-dai wurinta ya saka SHAREEF ya buɗe mata cinyanta, after ya buɗe ya tsira mata alluran zuwa jikinta A ɗan ƙanƙanin lokaci ta dena mutsu-mutsun da take yi, sai numfarfashi da take faman yi ta nanƙwaye kanta ta sama ta sanƙare a jikin SHAREEF ɗin, still har yanzu jinin da ke zuba a hancinta yana ɗiga a yanzu kaɗan-kaɗan, sai shaƙuwa take yi idanunta suna koma wa fari kamar ranta zai fita, sai kuma baƙin idanun su dawo dai-dai haka suke yi, duk fuskarta zuwa jikinta ya ɓaci da jini, duk wanda ya riƙe ta sai da ya samu jinin ya ɓata shi, musamman SHAREEF da farar rigansa tayi sharkaf Likitan yace mishi, "ya ɗauke ta zuwa kan gadon ya ɗaura ta." Hakan kuwa yayi daƙyar ya ɗauke ta, amma abun tausayin duk jikinta ya kanannaɗe, yatsun hannayenta sun yi kamar na kuturwa bakinta a karkace, haka kafafunta a nanƙwaye har da mai ciwon, Duk yanda suka so su miƙar da ita sun kasa, Ƙarshe dole suka barta a hakan har suka jira Malamin ya zo, ita kuma har lokacin barcin bai ɗauke ta ba tana nan a yanda take tana nishi da fitar da ƙara mai ƙarfi, sai ta saka ƙara sai kuma can tayi lagwab ta koma fitar da gurnani Ba su Momy kaɗai ba, hatta Likitocin hankalin su ya tashi da ganin halin da take ciki, sun tausaya mata matuƙa don daga gani tana matuƙar jin jiki; har da masu zubar mata da hawaye, abun gunun tausayi Sai da Malamin ya zo sannan aka samu aka sauko da ita tunda shi ya bada umarnin a mayar da ita ƙasa, Sannan ya zauna dukkansu suma suka samu wuri suka zauna suna kallon yanda ya soma mata karatu, a wannan halin ya jima yana mata karatu yana tofa mata addu'o'i waɗanda suka soma tasiri a jikinta Nan take ta fashe da kuka tana ƙara mai firgitar wa, jikinta ya ci gaba da kanannaɗe wa kamar kuturwa Malamin ya saka aka riƙe ta ya ci gaba da mata karatu tsawon lokaci, Tukun suka samu ta soma magana bayan Aljanin kanta ya hauro kanta Cikin kuka take sambatu da maganganu cikin tsananin wahala da wani irin gurnani, ta soma zayyane musu abun da ke faruwa, a cewar Aljanin, "wacce take son kashe ta suna son shanye mata jininta ne, amma sun kasa cin galaba a kanta, yanzu haka suna can suna tsaface-tsafacen su zasu kashe ta, amma bazai bar hakan ba, idan ba a taimaka an ceci Maryamu ba a koyaushe zata iya mutuwa in jininta ya ƙare, zasu kashe ta." Hankalin kowa a ɗakin ya yi ƙololuwar tashi musamman su Momy da suka fi sanin me ke faruwa, kuma a yanda suka ga ta jigata tana wani irin kuka da gurnani a yanzu jinin nata na zuba sosai Sai Malamin yayi saurin cewa, "don Allah ya faɗa musu komai domin su san ta yanda zasu yi su taimaka mata kar su ci galaba a kanta, su waye suke son aikata hakan a gare ta?" Nan fa Aljanin ya soma koro musu bayani tsab ya tona asirin Haseena da abun da take shirin aikata wa a yanzu Zuciyar kowa buga wa take yi sun tsorata da abun da Aljanin ke faɗa, abun tamkar almara, Amma Malamin tuni ya ci gaba da mata wasu addu'o'i ya dafe kanta yana ci gaba da tofa mata, An ɗauki lokaci kafin ya samu jinin ya tsaya kuma a nan take ta dena motsa wa sai dai numfarfashi da take sauke wa, Malamin ya sanya aka samo mishi ruwa ya ci gaba da tofa addu'o'i a ciki tsawon lokaci, sannan ya sanya SHAREEF ya shafe mata kaf jikinta da shi, A hankali komai nata ya soma dawowa daidai sai kuma kamar barci ya ɗauke ta; ta ci gaba da sauke nishi mai ƙarfi har da munshari, Malam yace, "ku ɗauke ta a mayar da ita gida don babu amfanin zamanta a nan; tunda an san matsalarta, abun da yakamata muyi yanzu mu san yanda zamu yi mu hana ita Matar aikata abun da take ninya, tunda ƙungiyar asiri ne a koyaushe zasu iya cin galaba a kanta su kashe ta, addu'o'in da nayi mata zasu taimaka mata sosai wajen tsare ta baza su taba cin galaba a kanta ba, amma insha Allahu yanzu zan koma gida akwai tanadin da zamu tashi musu tsaye domin ganin bayansu, dole ne a tarwatsa su idan ba haka ba zata cimma manufarta, ku ɗauko ta mu tafi." SHAREEF shi ya ɗauke ta sannan suka fita har da Likitan ya bi bayansu, Aka bar sauran Nurse's din da suke wurin cike da al'ajabi da tausayin Maryamun, don dukkansu sai da suka zubar mata da hawaye, basu taɓa ganin abu makamancin irin hakan ba koda wurin masu aljanun ne, lallai wannan yarinyar tana shan wahala, jikinsu yayi sanyi matuƙa, kenan a koyaushe za a iya kashe ta tunda tsafi ake son yi da ita, lallai duniya abar tsoro ce, hankalin su ya tashi matuƙa jikinsu ya sake yin sanyi Har wurin Mota Likita ya raka su sannan yayi musu addu'ar samun lafiyarta yana sake ce ma Dady, "idan ta samu lafiya a kira sa a faɗa masa don Allah, ko don hankalin su ya kwanta, duk yanda ake ciki a faɗa mishi." Malam a gaba ya zauna tare da Driver, su kuma suka shiga baya suka wuce gidan, Bayan sun kai gidan; Drivern ya ɗauki Malam a bisa umarnin Dady ya wuce dashi gida, Su kuma suka shigar da ita cikin gidan aka kwantar da ita a saman Kujera, Dukkansu sun yi jugum sun kasa ma magana sai kallon Maryamun suke yi, Sai kuma Momy ta matsa ta ci gaba da mata addu'o'in tana tofa mata While SHAREEF na gefe idanu sun kaɗa sun yi jazur; ya kafe Maryamun da idanu amma a ransa baƙin ciki da tsanar Haseenan ne ya cika sa, yana son tashi ya je ya ɗauki mataki a kanta amma ba ya son jirgawa wurin Maryamu, domin gani yake yi kamar in ya tashi za a iya kiransa a ce mishi Maryamu ta mutu, Don haka yana nan manne da ita ya gaza jirgawa Ana haka sai ga Hanif ya zo gidan gaishe ta, ya zo ya tarar da wani tashin hankalin da ya fi wancan, don Momy ta ba shi labarin abun da ke faruwa hankalin sa ya tashi matuƙa, yace, "gaskiya Dady a san abun yi kar yarinyar nan ta hallaka Maryam, ƙungiyar asiri kuma? Wannan ai babban tashin hankali ne komai zasu iya aikata wa, innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!" Ya hau salati cikin ruɗu Yayinda su Dadyn suke taya shi zuciyoyin su cike da ƙunci, Dady yace, "basu da matakin da zasu ɗauka a kanta amma komai zai zo ƙarshe insha Allahu, su jira Malam ya dawo su san mai za a yi, tunda ya faɗa musu za a iya karya ƙadarin ƙungiyar da ƙarfin addu'a, za a iya ganin bayansu." Sai ga driver ya shigo a lokacin ma, da saƙon Malamin da ya tsayar da shi ya ba shi wani magani a kwalba mai ƙamshin gaske, yace mishi, "a shafa mata yanzu a dukka jikinta." Malamin ma sai ga kiran nasa ya shigo a wayan Dady, bayan ya amsa ya sake mishi bayani sosai sannan yace, "su kasance da addu'a dukkansu, itama su ci gaba da mata suna tofa mata, yanzu haka ya tara almajirai da wasu malamansu zasu tashi tsaye wurin musu addu'a don ganin bayansu, insha Allahu kafin dare komai zai zo ƙarshe, in har basu bar yarinyar ba dukka sai sun shiga bala'i don baza su taɓa samun sukuni ba, zasu rusa ƙungiyar tasu". [11/05, 9:10 PM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE37* _____Cikin ƙuduran Allah bayan an tashi tsaye wajen duƙufa da karatu da addu'ar karya ƙungiyar; tun a wannan daren mai afkuwa ta soma afkuwa, wanda sanadin haka Allah ya fara tona musu asiri, abun ya faru ne a lokacin da suke tsaka da yin meeting din su, wanda nan take gobara ta tashi ayar Allah ta soma tasiri a kansu, duk yanda suka so suyi wani abu mai kama da sihiri sun kasa, Lokaci guda sai ga wasu daga cikin jami'an tsaro sun farmaki wurin nasu, dama sun sha kawo farmaki sabida abubuwan da ake faɗa a wurin da jita-jitan da suke samu, ko sun zo basu taɓa ganin kowa a wajen ba sabida an yi amfani da sihiri ba wanda zai ga mai ke faruwa a wurin, babban fili ne wanda aka kewaye wurin da bishiyu, a nan ne ƙungiyar asirin nasu take, majority a baya idan an so ganin bayansu ba a samun damar hakan, wanda ma yasan zancen ƙungiyar nasu rasa ransa yake yi, sai ga shi Allah da ikonsa sanadin ɗauke wani Yaron mai kuɗi da aka yi, sai aka kama mutumin batare da ya ida nufinsa a kan Yaron ba, Mahaifin Yaron kuma sai ya ɗauki mutumin ya danƙa shi a wurin hukuma, da aka matsa shi da duka da bincike, sai ya bayyana komai, kuma suka taso ƙeyanshi don ya kawo su wurin, A kuma dai-dai nan saboda Allah ya so ya ga bayansu, addu'ar Malaman da suka wuni suna yi Allah ya amsa, Wannan dalilin ne wajen ya fara kama wa da wuta sabida bom din da jami'an tsaron suka saka, sannan suka shiga suka yi musu rubuti kan mai uwa da wabi suka dinga duka suna kashe wasu, yayinda suka so yin amfani da tsafin su wajen tsira amma abun ya cutura, Ƙarshe an kama wasu; wasu kuma an kashe su a nan take batare da an tausaya musu ba, aka rusa wurin gaba ɗaya aka yi baja-baja da komai Kafin ka ce me; ƴan jaridu sun cika wurin ana ta ɗaukar rahoto, tun a daren labari ya soma yaɗuwa a kan wannan mummunar ƙungiyar asirin da yau aka ga bayan su, labarin da ya yaɗa kaf ƙasar Australia da ma kewayen ta, ana ta haska wa a TV da jaridu A washe garin ranan ne Abba da ya tashi zai yi tafiya, ya je duba Haseena don ya sanar mata tafiyar nasa tunda ya jira - ya jira bata fito ba, amma abun mamakin ko sama ko ƙasa babu ita; daga ita har ƙawarta Nana, an duba gidan ko'ina babu su a ciki, kuma Mai gadi ya tabbatar wa da Abba, "basu fita gidan ba." in fact ma bai buɗe gidan ba sai da asuba lokacin da Abba zai je masallaci, shi kuma yana wurin a nan yayi Sallah tunda haka yake yi sabida gadin gidan, Abun ya ɗaure wa Abba kai, yayi ta kiranta a waya ko zai same ta amma babu labarin ta tunda wayan ba ta shiga, Abun kamar almara kuma kamar wasa; zance ya zama gaskiya, tunda karshe da ya ji shiru bata dawo ba dole ya ɗage tafiyar zuwa gobe, Amma kuma babu ita babu labarin ta, abun ya soma tsorata shi hankalin sa yayi matukar tashi, sai ya koma bin dangi yana neman inda zai ga Haseena, In takaice muku zance har gidan su SHAREEF sai da Abba ya je wai neman Haseena Su kuma ɓatan Haseenan bai basu wani mamaki ba, sabida bayanan da Malam yayi musu a kan ƙungiyar, ya rigada ya bayyana musu cewar, "dole ƙarshen su ya zo, dole sai wata fitina ta afka musu sai sun tarwatse." Suna ganin cewa hakan yana da nasaba da addu'ar da aka yi musu, Fatan su dai Allah yasa hakan ne don a yanzu burinsu kawai Maryamu ta samu lafiya, But har yanzu dai shiru ne babu ci gaba a lamarin ta, tana cikin wani hali gaskiya, wanda idan bawa ya kalle ta sai ya tausaya mata, sai ya zub da mata da hawaye, sai ya koka mata, A kullum hankalin su a mugun tashe yake, babu wanda ba ya zubar mata da hawaye, abun ya cutura don gani suke yi kamar zata mutu ne, wanda hakan yasa dole Dady ya kira iyayenta ya sanar musu, don kar ya zo ta mutu a hannunsu cikin wannan ciwon batare da sun sani ba, hakan bai yi musu adalci ba, ya faɗa musu iya abun da zai iya faɗa musu, daga ciwon da take yi na aljanu har izuwa yanzu da ciwon da ya dawo mata gadan-gadan kullum suna kanta aljanun Gaskiya bazan iya misalta muku halin da iyayenta suka shiga ba, amma a ranan sai ga su sun shigo Kano, sai dai tun a kallon da suka yi mata na farko hankalin su ya ƙara tashi fiye da halin da suke ciki, Inna kukanta ta kasa riƙe wa tana mamakin wai Maryamu ce ta koma haka? gaba ɗaya ta firirice ta gama fice wa a hayyacinta, idan tana wani abun tamkar mara hankali, har yanzu ƙafanta da ta kumbura har yanzu tana nan a haka sai ma ɗuran ruwa da tayi, abun kamar zai yi sauƙi sai kuma ba haka ba, kuma wai don an dage mata da neman magani ne, iya ƙoƙari ana yi a kanta gaskiya shiyasa ake samun sauƙi, da tuni ba wannan zancen ake yi ba Baba dai kasa haƙuri yayi yace, "a ba shi ƴarsa ya tafi da ita gida, a can zasu yi mata magani." Dady ya so ya ba shi haƙuri tunda ga shi ana samun ci gaba fiye da baya, abun ne idan yayi gaba sai kuma yayi baya, ya faɗa masa, "yayi haƙuri tunda a nan sun san mafarin ciwon nata, Malamin da ke duba ta yana iya ƙoƙarinsa ana dace wa." Tunda aljanun kanta ne suka hana ta sukuni, kullum sai sun tashi mata, shi aljanin yana son wai sai an ba shi Matarsa, sai an sake ta SHAREEF kuma ya ƙi sakinta duk da ganin halin da take ciki, don shi ya fi ta ma shiga wani hali, bare da ya ji maganar Baba da yake cewa zai tafi da ita, hakan ne yasa yace mishi, "babu inda za a je mishi da Matarsa, a barta a nan tunda shi ne Mijinta, idan ya raina ƙoƙarin su ne ya je ya kawo maganin a yi mata a nan, amma bazai ɗaga mishi Mata ko nan da can bane." Dady ne ya daka mishi tsawa yana cewa, "baka da hankali ne SHAREEF? Shi da ƴarsa ka ce bazai tafi da ita ba? Ina ka taɓa jin an yi haka?" Hawaye kwance a idanunsa yake cewa, "Dady ai ko shine Mahaifinta; Ni kuma Mijinta ne, ina ga ya raina ƙoƙarin mu ne shiyasa yake son tafiya da ita..." "Rufe min baki dalla can, in ƙara jin ka sake magana a nan." Dady ya faɗa a tsawace a kuma fusace yana hararan SHAREEF ɗin Shi kansa Baba sai yanzu ya ji bai kyauta ba har ransa, sai yace, "kuyi haƙuri don Allah, hankalina ne ya gushe sabida halin da na tsinci ƴata a ciki, na san Mijinta ya fi Ni iko da ita, don haka bazan ɗauke ta ba zan barta a nan ɗin, Allah ya bata lafiya." "Amin Amin." Suka amsa su dukka, Yayinda Dady ya sake ba shi haƙuri yana ƙara jaddada mishi, "insha Allahu zasu yi iya yin su, ko ina zasu je domin nema mata lafiya, yayi haƙuri ya barta a nan komai zai wuce da yardan Allah." To dalilin da yasa aka bar Maryamu a nan kenan ana kula da ita, Wanda sabida yanayin jikin nata ne yasa su Inna sai da suka yi kusan sati ɗaya before suka koma cike da tausayinta da tunanin halin da take ciki Haka rayuwar ta ci gaba da gudana, a halin yanzu itama Amra rashin lafiyar yasa an mayar da ita gaban mahaifiyar ta, tunda tun cikin da ta samu take faman laulayi mai matuƙar wahala, ga shi har lokacin babu ci gaba a samun lafiyarta, har Hanif ya yanke shwaran fita da ita ƙasar waje, sai kuma ciwon Maryamu ya dakatar dashi, sannan kuma daga baya sai itama ta soma ciwon Momy tace, "ya ɗauke ta ya mayar da ita gidan su sabida zasu fi kula da ita, tunda ciki ne zata fi samun kula wa wurin Mahaifiyarta." Hakan ne yasa aka mayar da ita gida, yanzu kusan watanni uku kenan tana can har lokacin jikin babu daɗi, sai an dawo da ita kamar ta warke, kasancewar Afra take zaune da ita, sai kuma jikin ya sake rikicewa dole aka sake mayar da ita wurin Mama, ga shi irin cikin nan ne mai shegen tsirfa ga laulayi, ga babu damar tayi wani aiki, to ina ta ga wani lafiyar bare tayi wani aiki? Tunda tuni Likitoci sun hana ta ɗaukan komai koda tsinke ne, a cewar su, "cikin bai da ƙwari zai iya zube wa". *** *** *** _____Har wannan lokacin babu labarin Haseena tunda aka neme ta aka rasa, tun su Abba suna saka ran dawowarta har sun fidda rai, kuma ko kusa babu wanda ya ji labarin abun da ke faruwa duk da an haska a yawancin talabijin, dayake labarin ne kawai da inda abun ya faru, babu fuskokin jama'ar da aka kama Sai kwanan nan bayan an rufe su tsawon lokaci ana gana musu azaba kala-kala, wanda ya jawo mutuwar rayuka da dama, kwatsam...! sai suka ɗaura wa sauran video kowacce tana bayani da kanta da dalilin shigowarta harkan, da kuma abubuwan da suke aikata wa a ciki, Wanda ciki har da Haseena da ita tana raye bata mutu ba, Nana kuwa tun gana musu azaban da ake yi wani irin ciwo ya kama ta na tsananin wahala, daga nan kuma sai wasu tsutsotsi suka dinga fito mata a ƙasanta sakamakon rashin samun biyan buƙata kamar yanda suka saba, ciwon yayi mata tsanani ga azaban da ake basu, lokaci guda zuciyarta ta buga ta mutu a nan take, sai warin ta aka ji, Sauran ma suna a cikin yanayin da take ciki, Dukkansu tsutsotsin suke fita a cikin jikinsu ga wari da suke fitarwa, rashin samun junan su ne yasa hakan take faruwa, wanda wasu har sun yi dabara sun soma biyan buƙatar su tunda a haɗe suke, Da jami'an suka sani sai suka raba su kowacce da ɗakin ta, suka kuma ci gaba da gana musu azaba kala-kala Kwatsam..! hiran da aka yi da su da nuna fuskokin su, ya jawo hankalin jama'a da ƙasashe da dama, wanda nan take labarin ya yaɗu har cikin Nigeria wasu daga cikin waɗanda suka san Haseena da yawa sun gane ta kuma sun santa, musamman ƴan uwanta, Bare labarin da ta bayar tana yi tana kuka, da yanda ta kashe ƴar uwanta da mahaifiyarta A BBC News an haska babu iyaka, wanda yasa har gidan su SHAREEF sai da suka ga labarin, sun yi matuƙar mamaki abun ya ɗaga musu hankali, duba da yanda rayuwarta ta koma babu kyan gani, ga halin da take ciki, a cikin su babu wanda ya ji tausayin ta barin ma SHAREEF, wanda shi hankalin sa a tashe yake da baƙin cikin kasancewar ya taɓa auren ta, tunda yanzu kowa zai kalle shi da abun ne waɗanda suka sanshi, sabida har a labarin nata ta saka shi a ciki komai na rayuwarta sai da ta bayyana Mutane sun yi turr da ita matuƙa, tunda har lokacin ita kanta baza tace ga dalilin aikata abinda ta aikata ba, wacce ta sanya ta a bala'in da kuma ƙawayenta su Herin duk sun mutu, kowa laifin Haseena yake gani da kuma mugun abun da ta aikata, babu kunya babu tsoron Allah, ga shi asirin su ya tonu, abun baƙin cikin ma tana ƴar Musulma Bahaushiya amma ta je wata ƙasa ta haɗe da wasu ƙabilu tana aikata abun da ta ga dama Sanadin hakan yasa Abba ya yanke jiki ya faɗi, tun ganin labarin abun ya firgita shi ya faɗi a nan take, aka yi dashi asibiti cikin halin ciwo. Komai yayi farko dama zai yi ƙarshe, karshen masu aikata saɓo kenan, wasu tun a nan duniya Allah ke nuna musu ikonsa. ***** A yanzu dai za a iya cewa jikin Maryamu da ɗan sauƙi ba kamar baya ba, amma kuma yanda itama take amai a koyaushe, hakan ne yasa aka kira Likita ya duba ta don su tabbatar da mai yake damunta, Kuma tashin farko aka gane tana da shigan ciki kusan watanni huɗu Abun ya ɗaure musu kai kuma ya saka su farin ciki, ai sai kuma baƙin cikin su yakau damuwa ta yaye farin ciki ya yaɗu, musamman Goga SHAREEF babu wanda yakai shi murna da ɗoki, Allah da ikonsa kenan! Mai yanda ya so da kuma miƙa kyauta a sanda ya so, ga shi a halin da Maryamu take ciki ashe har da ciki a jikinta, kuma duk wannan abun bai zube ba bare ya samu matsala, Wannan dalilin ne yasa suka ƙara bata kulawa na musamman, duk da a yanzu komai Alhamdulillah za a ce don hankalin ta ya dawo jikinta, ashe zafin laulayin ne itama yasa har yanzu tana jin jiki sosai, sai kuma kanta da koyaushe ƙorafinta kenan ciwo yake yi, Yanzu kafarta ta warke musul har taka wa tana yi wani lokacin in jikinta da ƙwari, Tun fara ciwonta shima SHAREEF ya dawo gidan da zama, a ɗakin da take kwana a nan yake kwana yana kula da ita, komai take so shi yake mata har wanka da duk wani kula shine mai yi, sai wani lokacin ne Momy take taimaka mishi amma ba ya jirga wa, aikinsa kuwa tuni ya ajiye sa ba ya zuwa, don ma Companin Dadyn su ne; da tuni an kore shi Hanif ne kawai yake zuwa, shima yanzu komai normal a wurin su tunda Amra ta samu lafiya ta koma gida sai godiyar Allah sai kuma abun da baza a rasa ba.           Bayan wasu lokuta jikin Maryamu ya murmure sosai, cikinta har ya fito yayi girma, yanzu komai alhamdulillah za a iya cewa tunda a halin yanzu jiki yayi kyau matuƙa, duk da har yanzu ba kasafai wani lokacin take samun lafiya ba, kan nan nata yana matuƙar matsa mata, shi ne dalilin da yasa har yanzu ake mata magani, amma sarai ta warke, don har gida ake kiran wata Likita Mace tana duba ta sabida cikin nata Kasancewar SHAREEF akwai zafin kishi, don haka da kansa ya nemo Mace ita take kula da ita, sai kuma Malamin da ke bata magunguna ana shafa mata ko ta sha wasu, yanzu haka burinsa kawai Maryamu ta koma gidansa, amma su Momy sun hana sun ce, "ya barta a nan har ta haihu." Shi kuma gaskiya yana takura don yana son bata kulawa matuƙa, amma ba ya samun damar hakan, yawanci Momy tana wurinta ko kuma a fita da ita Falo suna zaune tare a can, ga idon jama'a tunda ana yawan zuwa gaishe ta musamman ƴan uwan Momyn, kwata-kwata bai samun yanda yake so, burinsa ya bata kulawa ya ririta ta kamar ƙwai, Don haka ya nace wa Momy dole sai an ba shi Matarsa Momy tace, "to ka ɗauke ta tunda baka da kunya, babu inda Maryam zata koma har sai ta haife abun da ke cikin cikinta lafiya; sannan kake da damar daukar ta, ya za a yi cikinta ya soma tsufa kuma ka ɗauke ta ka kaita inda babu kowa?" Fuska ya kwaɓe yana cewa, "Mom, Ni ba mutum bane wai? Ni bazan iya kula da ita bane? Duk abun da take so Ni zan yi mata, kawai ki bani ita mu tafi gaskiya bazan iya jira har wani lokaci muna nan ba." Ware idanu Momy tayi a kansa tana kallonsa don ta kasa magana tsaban mamakin sa Yayinda Maryamu kuwa tana shan fruits ne, ƙafafuwanta a saman Centre table tana ta dariya Hakan ne yasa SHAREEF ya harare ta yace, "ke wai da wa kike yi ne ina magana kina min dariya?" Fuska ta taɓe itama tana buɗe mishi idanunta, sai tace, "Ni ba da kai nake yi ba fa, kallo nake yi." Sai ta tura baki gaba tana ɗage kanta zuwa kallon TV, yayinda ta ci gaba da shan fruits ɗin ta da Spoon Tasowa yayi ya dawo inda take, yana kamo hannunta ɗaya tare da marairaice fuska yace, "Baby ko ke ba kya son mu koma gida ne? In kika saka baki Momy zata yarda tunda kin ce min kina son zuwa, ke da bakin ki fa kika faɗa min haka." Jin haka sai Maryamu ta dube sa, sai kuma ta kalli Momy da ta zuba musu ido tana jiran ta ji abinda zata ce, sai kawai ta kwaɓe fuska tace, "wlh Momy Ni ban ce ina son zuwa ba, shine ya matsa min sai na faɗa miki mu koma wai za ki ji maganata, amma Ni ba na son koma wa nan ya fi min." "Ƙyale shi Maryam, ai na sani sai dai shi ya zuga ki." Sai ta banka mishi harara tace, "to ka tashi ka wuce tunda baza ka samu abun da kake so ba, Maryam dai baza ta koma ba sai ta haihu duk nacinka SHAREEF." Miƙe wa yayi duk ransa ya ɓaci sabida har yanzu ya kasa samun nasara, don haka yabar wurin yana kumbura baki, yana jin Maryamu tana masa dariya amma bai juya ba, kai tsaye saman ya haye ya je ya samu Dady a ɗakin sa, sai da ya shiga ya zauna before yace, "Dady please ka saka baki Momy ta bani Matata mu koma gidan mu, wlh Ni na gaji da zama a nan gani nake yi kamar ban yi aure ba, ta samu lafiya fa, kuma yanzu remain two months ko fiye da haka fa sannan zata haihu, gwara mu koma kawai." Baki Dady ya riƙe sabida jin kalamansa Shi kuma sai ya duƙar da kansa yana shafa ƙeya don sai yanzu ya ji kunya ta kama sa Sai Dadyn yayi murmushi yace, "just two months kake ganin baza ka jure ba My son? ai Momyn ka ta faɗi gaskiya, gani kake yi zaka iya kula da ita, baka san cewa abun da wahala ba musamman yanzu da cikinta ya tsufa; kuma ita ba ƙoshin lafiya ta cika ba, kayi haƙuri kawai ka barta a nan don baza muyi wasa da lafiyarta ba." "Dady, wai shi ba ga Hanif can da Matarsa a gida ba? Please Dady don Allah ka saka baki, i promise da zaran cikin ya shiga watan haihuwa zan dawo da ita, ina son gaskiya Matata a kusa dani kuma..." Sai kuma yayi shiru kamar zai yi kuka Dady kuma sai yace, "eh na ga alamun da gaske kake yi, kar kuma mu hana ka a samu wata matsalar daban, shikenan ka je zan yi mata magana za a baka Matarka." Dariya SHAREEF yayi, farin ciki yalwace a kan face ɗin sa don ya kasa ɓoye wa, yace, "thank you daddyna, Nagode sosai." Shi kuma Dady dariya kawai yayi yana kaɗa kansa, before ya ci gaba da abun da yake yi tunda yana duba jarida ne, After SHAREEF ya fita da ɗan wani lokaci before shima ya tashi ya shiga toilet ɗaura alwala, tunda an kira sallan Magriba Dady da kansa ya yi wa Momy magana yace, "zuwa gobe kawai a mayar da Maryam ɗakin ta tunda yanzu komai ya wuce jiki alhamdulillah, inyaso kamar nan da wata ɗaya sai ta dawo, idan ba haka ba SHAREEF bazai barsu su sarara ba." Momy ta so ta hana tunda tace, "komin nacin sa a bar sa ya ci kansa." But Dady yace, "a ba shi kawai Matarsa su je suyi rayuwarsu su kaɗai, hankalin su zai fi kwanciya." Wannan dalilin ne yasa washe gari Momy ta je gidan aunty Najwa, suka haɗu a can suka wuce gidan Maryamu suka gyara mata gidan; su da kansu, ko'ina tsab sai da suka gyara suka goge before suka dawo Zuwa yamma kuma SHAREEF ya ɗauke ta a mota tare da sauran kayan ta suka wuce gidan sai jin dad'i yake yi, ko banza ai yanzu zai bata kulawa kamar yanda yake buƙata, don a nan yana takura bai samun yanda yake so in har ba da dare bane suka kwanta tare, da zaran safiya tayi kuma sai wani daren, don haka a takure yake matuƙa. _Happy juma'at fans. Enjoy your weekend._ [15/05, 6:39 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱        *SHAREEF*            _SexyBoy_ 🌱🌱🌱🌱🌱 _Writer: Nafisat Isma'il Lawal_ _Wattpad: UmmuDahirah_ *Littafina na kuɗi ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.* __________ *BOOK2* _______________*PAGE38* _____ *A FEW MONTHS AGO* Tun a cikin Barcinta take jin kamar ana tsikarin ta a ciki, yanayin ciwon da yake damunta shiyasa gaba ɗaya ta kasa barcin mai daɗi, tun tana juyi ta haɗa zufa kashirɓan daƙyar take jan numfashi, can kuma sai ta farka sabida ta kasa samun sukuni mai daɗi, a hankali ta ci gaba da sauke nimfarfashi tana duban Hanif da ke ta sharan barcin sa abun sa, kasa tashinsa tayi; tayi shiru tana riƙe da cikinta sai murkususu take yi, dama tun daren jiya take jin yanayin babu dad'i daƙyar ta samu barci ya sure ta tunda shi ne a idonta, amma yanzu da ciwon ya ɗan ƙara yawa dole ta farka, Ta jima a wannan yanayin tana son koma wa wani barcin but ta gaza, fitsarin da ya matse ta shiyasa ta miƙe daƙyar ta nufi hanyar toilet, daƙyar take tafiyan sabida girman cikin nata, Kusan ten minutes ta ɗauka a ciki before ta fito, Sai dai tun a bakin ƙofan wani irin murɗaɗɗen ciwon ciki ya cafke ta, da sauri ta tamke cikin tana ƙoƙarin dafe bango amma ina ta gaza, salati take yi a cikin ranta tana mai runtse idanu har sai da takai ƙasa, kafin wani lokaci ta haɗa zufa kashirɓan sai karanta addu'a take yi a zuciyarta ko zata samu sukuni, amma abun babu sauki, ta san bazai wuce naƙudan da ake cewa bane tunda end ɗin ta yayi haka aka ce musu a asibiti, wannan azaban ciwon da ya farmake ta; ta sadakar haihuwar ce, ga shi lokaci guda ta soma galabaita don zama ta kasa yi bare zuƙunuwa, ta rasa inda zata saka kanta ta ji dad'i sai faman cije laɓɓa take yi, daga wannan lokacin ta kasa ɗaukar ƙafarta bare ta isa inda Hanif yake kwance, ga shi ba murya ce da ita ba balle tayi magana ya ji ta, wahalar da yayi mata yawa kawai sai ta fashe da kuka, ji take yi tamkar ana kunna mata wuta don azaba, wani irin murɗawa da cikinta ke yi gaba ɗaya ta kwanta a ƙasa tana birgima bata san ma tana danne cikin ba, sai kuka take yi tana shushshura ƙafa While Hanif bai san tana yi ba tunda barcinsa yayi nisa ainun, kuma ko sautin kukan ta da ke fita kaɗan-kaɗan ba ya ji, tunda sun ɗan yi nesa da juna Duk yanda ta so ta ja jiki ta isa inda yake but ta gaza, haka ta dauki tsawon lokaci a wannan yanayin cikin azaba da tsananin ciwo, babu mataimaki sai Allah, tuni jini ya tsinke mata, tun tana iya kokawa da nimfashin ta har sai da ya soma ɗauke wa a jikinta; tayi kamar ta mutu babu inda nata ke motsi, can kuma kamar ta farfaɗo ciwon ya ɗan lafa mata, sai tayi ƙoƙarin jan jikinta daƙyar har ta soma zuwa wurin gadon, Takai wajen amma ta kasa tashi bare ta taɓo shi, haka tayi ta miƙa hannu tana jan zanin gadon don ta samu ya tashi, amma har lokacin ba ya jin ta, wani irin kuka ta fashe dashi mai ban tausayi, ta dage da iya ƙarfin ta tana son ta fidda muryanta don ya ji ta; amma kwata-kwata sautin kukan ba ya jin ta, Zuwa wani lokaci kuma ciwon ya sake dawo mata gadan-gadan, nan da nan jikinta ya rikice jinin da ke zuban mata ya ci gaba da zuba kamar an fasa ƙwarya, azaban ciwon da take sha na tsawon lokaci tuni ta sume; sabida jinin da ya zuban mata ta dena gani daga baya ta sume gau Dayake lokacin suhabi ta gabato, kamar shuɗewar mintina talatin aka yi kiran sallan farko, can kuma da aka kira sallah na biyo before Hanif ya soma juyi zai tashi, tunda sallan yanzu a cikin kunnensa ake kira, tun kafin ya buɗe idanunsa ya soma laluba gefen nasa don ya taɓo Amra, sabida ya saba duk idan zai tashi sai ya laluba ta ya ji ko tana nan, jin babu ita sai ya buɗe idanun nasa yana duban wurin tunda akwai hasken wata kaɗan ya haska ɗakin, ganin babu ita sai ya soma salati yana addu'ar tashi daga barci, daƙyar ya miƙe zaune yana faman doka hamma idanunsa na son rufe wa, a hankali ya zura ƙafafunsa zai sauka daga kan gadon, sai ya ji kuma kamar ya sauke a jikin Mutum, da sauri ya duba wurin sai ya ganta kwance male-male a wurin, take gabansa yayi mugun bugawa ya ƙarisa zuro ƙafafun da mugun sauri, "Amrah." Ya kira sunanta da ƙarfi da ya durƙushe a gabanta yana taɓa ta, jin kamar ba ta motsi sai yayi saurin ɗago ta yana sake kiran sunanta hankalin sa ya soma tashi, Bai tashi shiga tashin hankali ba sai da ya ji kamar danshi a wurin, koda ya dauko wayansa ya haska ta da kyau sai ya ga alamun jini ne, ya kasa yarda sai da ya kunna glop ɗakin ya gwauraye da hasken NEPA, a take hankalin sa yayi mugun tashin fiye da yanda ba kwa zato, ya ruɗe gaba ɗaya sai faman kiran sunanta yake yi yana jijjiga ta kamar mahaukaci, daƙyar ya ɗauke ta yayi ƙoƙarin fitar da ita cikin bedroom ɗin ko riga bai sa a jikinsa ba, daga shi sai gajeren wando, haka ya sungume ta daƙyar cikin ruɗe wa ya fitar da ita waje, cikin mota ya nufa da ita sai dai babu key, dole ya ajiye ta a wurin ya koma a guje ya dauko waya da key ya fito, yana zuwa ya buɗe motan ya saka ta a baya before ya ɗauki goran ruwa da ke cikin motan ya zirara mata yana fatan farkawar ta Kamar tana jira ya watsa mata ruwan ne sai ta kawo nimfashi nan take Hakan ba ƙaramin faranta masa rai yayi ba, take ya soma shafa fuskarta yana kiran sunanta zuciyarsa kamar zata tsinke don tashin hankalin da yake ciki Ita kuma ta ja nimfashi tana buɗe idanunta zuwa gare sa, nan fa ta fashe da kuka tana ƙoƙarin buɗe baki tayi magana amma ta gaza, sai haki take yi tana mirgina kai sabida zafin da ke ƙara huro mata Shi kuma tuni ya soma magana yana bata haƙuri cikin tausaya wa, yana faɗa mata, "yanzu zai kaita asibiti Insha Allahu zata samu lafiya." Sai ya ƙarisa shigar da ƙafanta don ya kulle ƙofan Amma sai ta riƙe masa hannu gam tana zubar da hawaye har da majinu, maganganu ne sosai a bakinta tana son faɗa masa amma babu hali, nan take ta ci gaba da kukan duk ta haɗa gumin wahala sosai sai tsiyaya take yi Hannunsa ya janye kamar zai yi kuka yana mai rufe ƙofan da sauri, don gani yake yi idan ya ci gaba da zama zai ɓata lokacin sa a nan wajen ne, ga shi itama kuma wahala take sha, Sai da zai shiga motan ya ankare bai da riga daga shi sai gajeren wando, kuma bazai iya fita a haka ba dole da gudun sa ya koma ya ɗauko jallabiya; ya zura a jikinsa yana jan Motan a guje ya nufi bakin gate yana danna horn da ƙarfi Mai gadi dayake ya tashi tunda an kira sallah, bai rigada ya fito bane, jin horn sai ya fito da gudun sa yana ganin Hanif ne ya je ya buɗe masa gate ɗin Shi kuma ya ja ya fice a gidan sai asibiti, a cikin motan ya kira numban Dady yana shaida musu halin da Amra taka ciki, yanzu ma haka asibiti zai kaita Don haka Dady yace mishi, "suna nan tafe Insha Allahu yanzu." Koda ya isa asibitin; shi da kansa ya fito ya buɗe motan ya ciro ta, daƙyar ya ɗago ta ya fito da ita ya nufi cikin asibitin, wanda babu kowa a haraban asibitin mutane da dama suna kwance, wasu kuma sun tashi basu fito ba, Direct hanyar ɗakin haihuwa ya nufa yana kwaɗa kiran nurses ganin babu kamar mutane a ward ɗin Ai kuwa tun kafin ya isa wurin ma sai ga wata nurse ta fito sabida jin kamar ana kiran sunayen su, Ganin Hanif sai ta nufi wurin sa da sauri tana tambayarsa lafiya? "Nurse taimaka mata Please, ciki ne, ina tunanin zata haihu ne." Nurse din ganin yanda Amra ta jigata tamkar bata da rai duk ta fita a hayyacin ta, ga kuma jini da ke zuban mata duk ta ɓata hanyar da suka fito, Shi yasa ta taimaka masa cikin sauri tana yi tana ƙwala kiran sunan wata Abokiyar aikinta Fitowar ta yasa suka taimakawa Amra zuwa dakin haihuwa aka shigar da ita, Sannan ɗaya ta nufi Office ɗin Likita da gudu tayi kiran ta Sai da Likitan ta zo ta tarar da Hanif cikin ɗakin yana tsaye gaban gadon Amran yana mata sannu, duk ya gama diririce wa daga shi har ita sun fice a hayyacin su, Dayake ta gane sa tunda a nan yake kawo Amran awo; kuma ita take duba ta, don haka ta kira sunan sa tana tambayar sa halin da ta shiga? Nan ya fayyace mata komai yana sanar mata, "shima ya tashi ne ya ganta a wannan yanayin, but bai san lokacin da ta soma naƙudan ba." Likitan sai ta bukaci, "ya fita zuwa waje zasu duba ta." Dole ya fita ba don ya so ba, yana ta sintiri a bakin ward ɗin har sanda ya ji kiran wayan Dady, da ya duba ya ga shi ne sai ya amsa call ɗin ya sanar masa inda suke Ba a fi minti biyar ba suka ƙariso wurin shi da Momy, hankalin su a tashe yake gaskiya don haka suka hau tambayarsa halin da Amran take ciki? Ya sanar musu, "an shiga da ita ana duba ta." "To Allah ya raba lafiya, amma hankalin mu ya tashi Allah ya sauke ta lafiya, baka sanar da Mahaifiyarta ba ko?" A cewar Momy da ke maganar cikin tsantsan damuwa Shi kuma yana share gumin fuskarsa yake gyaɗa mata kansa, yace, "a'a, ban sanar musu ba, Dady kawai na samu damar fada mishi." Dady yace, "to kira maza ka sanar da Mamansu, gwara su zo nan su san halin da ƴarsu take ciki ko zasu taya ta da addu'a." Hakan ne yasa Hanif yayi kiran numban Mama ya shaida mata, "suna asibiti yanzu haka Amra zata haihu." Kusan mintina ashirin sai ga likita ta fito duk fuskarta a dame, da alamun akwai matsala koda suka hangi face ɗin ta, ilai kuwa nan take shaida musu, "gaskiya naƙudan yayi nesa da yawa, akwai sauran awannin da yakamata takai before ta haihu, amma ta rigada ta galabaita already jininta ya zuba da yawa, kuma ana buƙatar ta samu ƙarfi gaskiya idan ba haka ba baza ta iya haihuwa da kanta ba, don haka za a ƙara mata jinin yanzun nan." Sosai suka ƙara shiga tashin hankali, dukkansu salati suke yi zuciyoyin su na cike da tausayin Amra Hanif ne yayi saurin cewa, "idan da hali; a je a duba nasa in zai yiwu a ɗiba a ƙara mata." Likitan tace, "to ba damuwa su je." A tare suka tafi dashi da ita Ko kafin su dawo su Mama sun zo ita da Afra da Salma dukka suka taho, suma kansu hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba, musamman da suka zo Momy take musu bayanin halin da ake ciki, "yanzu ma haka an je gwada jinin Hanif ne za a ƙara mata, mu ci gaba da taya ta da addu'a Allah zai sauke ta lafiya Insha Allahu." A can kuwa ɗakin haihuwar Nurse ɗaya aka bari tana kula da Amra wacce duk ta gama fita a hayyacin ta, Nurse din sai mata sannu take yi tana ɗan danna mata ciwon don ta samu relief Ita kuma ciwo da azaba ya hana ta sukuni, don ji take yi tamkar za a ɗaɗɗake mata bayanta da Kwankwason ta, numfashinta daƙyar yake fita, bata kuka amma hawaye sai gudun tsere yake yi a idanunta, tayi waja-waja ta jigata tamkar wacce tayi kwana biyu tana naƙudan, a ranta ji take yi tamkar baza ta iya kaiwa anjima da rai ba, yadda take jin ciwon na sukanta tana jin kamar mutuwarta ya kusanto ta ne, burinta kawai ta sanya Hanif a idanunta, tana son faɗa masa wasu kalmomi da ke ranta sai dai babu bakin magana, hakan ne yasa ta fashe da wani irin kuka mai cin rai sabida babu halin ta sanar da Nurse abun da take so, Can kuma sai ta ɗago tana kallon Nurse bayan da ta ji ciwon ya ɗan lafa mata, daƙyar take iya ganin ta ma sabida hawayen da ke gudu a idanunta, nan ta soma mata bayani da hannu tana nuna mata tana son abun rubutu, sai kwatanta mata da hannu take yi cikin kuka Ita kuma Nurse bata gane ba sai faman tambayarta take yi, sai kuma daga baya kamar ta gane tace, "rubutu kike so ki yi?" Da sauri ta jijjiga mata kanta tana ƙoƙarin miƙe wa, duk da daƙyar take iya motsa jikinta saboda azaba Da sauri ita kuma Nurse din ta ciro memo a jikin aljihun riganta, Allah yasa akwai har da Bairo sai ta taimaka mata ta tashi zaunen; ganin tana ƙoƙarin zama ne, sannan ta miƙa mata tana sake mata sannu Daƙyar ta riƙe Bairon ta soma rubutun cikin rawan jiki, gaba ɗaya kuka kawai take yi tana rubutun zuciyarta a karye take sabida a halin da take ciki, tana jin a ranta baza ta iya rayuwa ba, tana buƙatar barin ma Mijinta wasiyya, don haka ta rubuta, "don Allah Mijina ka yafe min, ba na jin ciwon nan zan iya tashi sabida yanda nake ji a jikina, amma in har ban fito da raina ba ka yafe min abubuwan da nayi maka, na so nayi rayuwa da kai mai tsawo sabida in saka maka da abun da kayi min, amma.." sai ta yanke daga nan ta ƙara da faɗin, "idan na haifi abun da ke cikina ya rayu, don Allah ka bama ƴar uwata Afra kyauta domin na mallaka mata halak malak, kuma don Allah ka aure ta ta cike maka gurbina cikin zuciyarka, ina sonka Yaya Hanif." Daga nan ta dakata da rubutun sabida ya ci ƙarfinta, mika wa Nurse din tayi sai dai bata da bakin da zata iya mata bayanin wanda take so ta bata Ita kuma kamar ta sani sai ta soma tambayarta tana lissafa mata wa za a ba? Iyayenta ta soma ambata amma Amra ta girgiza kanta, tana cewa, "Ko Mijinki zan ba?" Da sauri ta gyaɗa mata kanta cikin halin ciwo tana riƙe ƙugunta Hakan ne yasa Nurse ta tusa takardan a aljihu tana mai riƙe ta ta ci gaba da mata sannu Babu jima wa Likitan ta zo tare da wata Nurse da ke rike da ledan jinin guda biyu, Nan aka soma ƙoƙarin ɗaura wa Amran While itama kuma wacce ta ba takardan sai ta fita da sauri don ta duba Hanif ta miƙa mishi takardan, ganin babu shi cikin su Dady dole ta dawo cikin dakin suka ci gaba da taimaka wa Amran, Tunda a lokacin Hanif ɗin yana ɗakin da aka ɗiba mishi jinin, Likitan tace masa, "dole sai ya ɗan huta before ya taso." Shima SHAREEF yana cikin su don a yanzu ya ƙariso, dole a yanzu ya taho yabar Maryamu tunda already tana gidan su Momy a yanzu, itama cikinta ya shiga watan haihuwa, kuma akwai su Yusaira sun zo hutu, don haka ya barsu a tare ya zo asibitin, Duk suna waje sun yi cirko-cirko babu wanda ya jirga a wurin; sai Dady da ya je yayi sallan asuba ya dawo Su Momy kuwa sai daga baya ne ma suka je suka yi tunda sun ji shiru har yanzu ba a fito musu da wani bayanin ba Gaskiya ba ƙaramin wahala Amra ta sha ba a wannan halin da take ciki, haihuwa ya ƙi zuwa duk ɗiba mata wannan awannin da suka yi, kuma shiru kamar an shuka dussa, sannan ga shi duk da jinin da aka ƙara mata dogon naƙudan yasa duk ta gama galabaita nishi ma dakyar take yi bare tayi wani yunkuri, Abun ya ɗaga wa kowa hankali, tun asuba ake abu ɗaya ga shi har kusan la'asar yanzu, sumanta uku sai numfashin ta ya ɗauke sai ya dawo can kuma, Su Dady ne kaɗai suke fita asibitin su je su dawo, don shima SHAREEF koma wa wajen Maryamu yayi tunda ta kira sa ta ɗaga mishi hankali, tana ta kukan shagwaɓa wai, "dole sai ya kawo ta ta ga Amra." Ya rarrashe ta ta ƙi haƙura, shiyasa ya tafi can wajen ta Hanif kuwa ba ya jirga wa a asibitin ko kaɗan, yana nan yana ta faman yi mata addu'a hankalin sa ya fi na kowa tashi a wajen, har hawaye yake zubar wa a ɓoye sallah kaɗai ke tayar dashi Daga karshe dai likitocin sun nemi a sanya hannu a yi mata aiki, tunda suna ganin hakan shi ne maslaha, dama already haihuwar fari yawanci yana kawo matsala da dama, wasu rashin buɗe wa ne da kuma wahalar da suke gamuwa dashi wanda ya fi ƙarfin tunanin su, ga tsoron da ke tattare da su, shiyasa sai su kasa haihuwa da kansu, don haka Amra dai ba sa tunanin zata iya haihuwa da kanta gaskiya, Shiyasa suka nemi Mijinta ya sanya hannu za a shigar da ita ɗakin Theatre A lokacin da aka basu damar su ganta gaskiya sun tausaya mata matuƙa, don ba ta iya bambance ma mutane sabida wahalar da take sha, kallonsu kawai take yi tana motsi da bakinta tana hawaye, amma kwata-kwata ba ta a cikin hayyacinta Su Afra sai kuka suke yi sabida halin da suka ga yar uwansu, don har su an shiga da su sun ganta, Kowa sai addu'a yake mata yana fatan a fito da ita lafiya Hanif kamar bazai sake ta ba daƙyar ya bari aka kaita ɗakin da za a yi mata aikin, yana nane da ita har sai da aka tashi yin aikin before a ba shi umarnin fita A sannan ne Nurse din nan ta zo ta ba shi takardan da Amra ta rubuta, don ita kanta ta manta kai ya ɗauki zafi sai yanzu da ta ganshi, don haka ta rugo a guje tana mishi magana, Bayan ya tsaya take ce mishi, "kai ne Mijin Matar nan ko?" Kai ya ɗaga mata idanunsa sun yi jazur sun fice a hayyacinsu, don a lokacin yanda yake ji a ransa bazai iya yin mata magana ba, shi kansa ji yake yi kamar Amra zata tafi ta bar shi, don jikinsa yayi sanyi a halin da ya ganta, ciwon nata yayi worst Takardan ta ciro daga cikin aljihun riganta, wanda tun lokacin da Amran ta miƙa mata ta saka shi a ciki bata buɗe ba, ta miƙa mishi tana cewa, "ita ta rubuta wannan da hannunta, ban san dai mai ta rubuta ba amma tunda kai ne Mijinta shiyasa zan baka, ita tace in baka." Hannunsa har rawa yake yi wajen miƙa hannu ya amsa, amma sai ya dakata sabida yanda ya ji zuciyarsa tana buga wa yana jin wani irin yanayi yana baƙuntarsa, daƙyar ya idasa miƙa hannun ya amsa, Sannan ya damƙe takardan ya juya ya tafi zuwa inda sauran jama'ar ke zaune, Wuri ya samu ya zauna ɗan nesa da su yayi shiru ya kasa buɗe takardan, daga ƙarshe kuma ya buɗe don ƙosawan da yayi ya ga abun da ta rubuta, Kansa ya dafe a sa'ilin da ya gama karanto rubutun da ta rubuta, wani irin harba wa zuciyarsa take yi kamar zata yi tsalle ta fito, hankalin sa yayi matuƙar tashi duba da yanda ya fahimci kamar wasiyya tabar mishi, hawaye ne ya soma gudun tsere a kan fuskarsa, sabida kar mutane su fahimci halin da yake ciki, sai ya kifa kansa a jikin ƙafafunsa a hankali yake furta, "a'a Insha Allahu baza ki taɓa tafiya ki bar Ni ba My Amra, ina sonki Allah bazai raba mu yanzu ba, Insha Allahu za ki fito lafiya.." Kukan da ya ci karfinsa shiyasa ya kasa ƙarisa zancen nasa, ya danne bakinsa yana kukan mara sauti, Yanayin da yake ciki yasa ya kasa kataɓus gaba ɗaya ya nemi ƙarfin jikinsa ya rasa, haka jikinsa ke rawa yana fatan a fito da Amra lafiya a ce masa bata mutu ba, Burin sa kenan a wannan lokacin Zuwan SHAREEF wurin, da maganar da yayi masa, shiyasa yayi saurin ɗago kansa yana kallonsa, yayinda hawayen kan fuskarsa suke sake gudun tsere idanunsa babu kyan gani saboda yanda suka koma SHAREEF ya rikice ganin halin da ɗan uwansa yake ciki, da sauri ya furta, "Hanif, mene ne haka kuma? Kukan mai kake yi a nan?" Kukan ne ya so kufce masa, amma sai ya dage ya tamke bakinsa yana mai lumshe idanunsa tare da ƙoƙarin saisaita numfashinsa Hankalin SHAREEF a tashe yake dubansa, ya kamo hannunsa duk ransa a jagule cike da tausayinsa yace, "don Allah ka kwantar da hankalinka Hanif, babu abun da zai same ta fa, aiki za a yi mata kuma lafiya lau zata fito da ikon Allah, idan ka shiga wannan wannan yanayin; baka san halin da su Momy zasu shiga ba suma, lafiya lau za a fito da ita Insha Allahu. Just prayer for her." Idanunsa ya buɗe yana kallonsa, amma sai dai har yanzu hawayen cikin eyes ɗin sa basu bar zuba ba, a tsorace yake a yanzu, a jikinsa yana jin kamar zai rasa Amra ne, don haka ya miƙa masa takardan yana mai faɗin, "ka ga fa abun da tabar min, taya ya hankalina zai kwanta bayan ta bar min wasiyya? ji nake yi kamar baza a fito min da ita a raye ba." Amsar takardan SHAREEF yayi ya soma karanta wa Ko kafin ya ƙarisa sai ga Likitan ya fito sun ji hayaniyar su Momy da ke tambayar Likitan, Da sauri suka tashi suma suna matsa wa inda suke domin jin halin da ake ciki Innalillahi wa'inna ilaihi taji'un! Tabbas Allah yayi alƙawarin kowa sai ya ɗanɗana mutuwa, before a yi wa Amra aikin ne sai ga haihuwar ta zo mata gadan-gadan, dayake rabo ne kuma shi Allah shi ke fitar da mai rai a jikin matacce, kafin mintina biyu kacal Amra ta fitar da abun da ke cikinta, kuma kamar ƙiftawar ido ko kafin ta buɗe idanu ta san inda kanta yake; Allah ya amshi abun sa Innalillahi wa'inna ilaihi taji'un! Rai baƙon duniya, tabbas bazan iya misalta muku halin da mutanen nan suka shiga ba, Amma nan take Hanif ya zube ƙasa yana fitar da wani irin numfashi mai wahala, kuka yake yi wanda ya sarƙe shi nan take ya sume a wajen Mamanta ma zube wa tayi ta sume gau a wurin, har Afra, Yayinda Salma ta rusa uban ihu tana kiran sunan ƴar uwanta Ihun ta da Salatin su Momy shi ya jawo hankalin jama'ar asibitin, kowa ya san babu lafiya a wurin Allah Sarki! Rai baƙon duniya, Tabbas makusantan ta sun ji mutuwar Amra ba kaɗan ba a wannan ranan, kowa kuka yake yi sabida rasa ta da kuma tsoron Allan da ya mamaye su Su Mama sun farfaɗo amma Hanif bai farfaɗo ba har aka haɗa gawan a asibitin aka bayar za a tafi da ita gida, Ikon Allah kuma Jaririn lafiya lau yana nan cikin ƙoshin lafiya sai tsala kuka yake yi yana neman abincinsa yana lashe baki, Ƙarshe dai a asibitin Likitan ta rubuta musu madaran da za a iya ba shi, tun a nan aka nemo aka fara ba shi ya soma sha Rai baƙon duniya, kowa yayi ɗammara don duniya to ya kwance, duk wanda ya zo zai tafi, mutuwa rigan kowa, babu wanda ya fi ƙarfin saka ta, basu da yanda zasu yi duk son da suke mata Allah ya karɓi abun sa, sai haƙuri, hakurin shi zasu runguma Ƙarshe dai halin da Hanif ya shiga a asibitin ya kwana don ya kasa tashi bare a je a yi jana'izar da shi, kuka ya dinga yi kamar ƙaramin Yaro, duk hakurin da ake ba shi abun ya cutura, Tunda Amra bata kwana ba tun a ranan aka rufe ta Maryamu bata da labari tunda mutanen gidan babu wanda ya dawo sai can dare suka dawo, SHAREEF kuma sai dai ya kwana a wurin Hanif, shi yake tausan sa yana ba shi haƙuri, To lokacin tayi barci bata san da dawowarsu ba, kuma ta sha kiran SHAREEF but bai sanar mata ba ya ɓoye mata saboda ganin halin da take ciki itama, Kamar kuwa ya san zata shiga wani halin, tunda a washe garin ranan ta ji Momy tana waya tana sanar da wasu daga cikin ƴan uwanta da basu sani ba, Ai a take ta ɗaga hankalin ta, bare dama tana da ciki itama haihuwa ko yau ko gobe, Allah Sarki! Sai jikinta ya rikice ta faɗi a nan tana kiran Cikinta Momy fa hankalin ta ya tashi, da gudu ta rugo wajenta tana kiran sunanta , tana tambayarta mene ne? Sai kuma ta koma kiran sunan Dady tunda bai rigada ya fita zaman makoki ba, kasancewar a can gidan su Amran ake yi Kiran da take mishi ne ya fito da Dady ya zo ya tarar da abun da ke faruwa, wani sabon tashin hankalin kuma, Ai babu ɓata lokaci suka wuce da ita asibiti, Amma a cikin su babu wanda ya faɗa ma SHAREEF sabida kar hankalin sa ya kara tashi, ana wata ga wata, itama ga Maryamu cikin wani hali, asibiti ɗaya kuma suke amma basu neme sa ba, don su kansu a halin da suke ciki tashin hankalin su bazai iya misaltuwa ba Momy har da hawayenta tana cewa, "innalillahi wa'inna ilaihi taji'un! Ya Allah ka tashi kafaɗan baiwar nan naka, kar kuma a maimata wani tashin hankalin, ya Allah ka sauke ta lafiya." Dady ya amsa yana cewa, "ki zauna don Allah a nan, addu'ar mu kawai take bukata, Allah zai bata lafiya. Zauna a nan kar ki faɗi." Zama tayi, shi kuma yana tsaye yana ta zagaye Kusan mintina talatin Likitan ya fito a ruɗe, wani abun mamakin sam sun nemi cikin Maryamu sun rasa, ita dai bata a cikin hayyacinta ta sume, amma kuma da suka duba cikin ko haihuwar ne, an yi scanning babu ciki amma ga tulelen cikin, abun ya ɗaure musu kai, kuma duk abun da zasu yi don su ga cikin but babu shi, Ikon Allah kenan! Bayanin da Likitan ya yi musu su kansu sun ruɗe, ba ƙaramin tayar musu da hankali yayi ba, amma duba da halin da take ciki na fama da aljanu sun san bazai wuce aikin su bane, innalillahi... Kenan har yanzu dai suna a tare da ita basu barta ba? Duk maganin da ake mata? Wannan wanne irin bala'i ne? Haka dai aka kira Malam tunda dai sun san bazai wuce wannan matsalar nata bane, bayan an kira shi aka sanar da SHAREEF shima, A lokacin ma Hanif jikin nasa da ɗan sauki amma har yanzu ba ya iya magana sai dai shiru yana faman tunani sai hawaye, ana ta mishi ƙarin ruwa don jininsa ne yayi mugun hawa, kuma bazai iya tafiya ba koda ya nemi a sallame shi ya koma gida Likita yace, "dole ya zauna na ɗan wanin lokacin tukunna." Sai ga shi kuma an kawo Maryamu asibitin, Itama Maryamun ta farka tana ta kuka sabida mutuwar Amran ya taɓa ta, abun ya bata tsoro musamman ganin itama tana da cikin, ta yiwu itama mutuwar zata yi, shiyasa hankalin ta ya tashi tana ta cewa, "a kira mata Iyayenta da Mijinta su gana, wataƙil mutuwa zata yi itama." Ta gaza kwantar da hankalinta duk yanda aka so a rarrashe ta Sai da SHAREEF ya zo ne sannan ta rungume shi ƙam tana kuka sosai da sambatu, abun gunun tausayi, don ma wai bata san halin da take ciki bane, Sai da Malam ya zo tukunna take jin abun da ke faruwa da ita, ai nan ta sake ɓarkewa da wani sabon kukan, ita kuma nata jarabtar kenan, daga wannan sai wanann SHAREEF ke ta faman rarrashinta yana faɗa mata, "babu abun da zai faru da ita da babynsu, za a nemo musu cikinsu." Shi kansa maganar yake yi kamar zai yi kuka don tashin hankali da rashin natsuwar zuciya Malam yayi musu bayanin, "sau da dama ana samun hakan, yawanci Aljanu ne suke sace cikin Mace sai a nema a rasa, wasu sai ya girma ta zo haihuwa sai a ga babu cikin, wasu kuma tun bai gama girma ba daga nan ya sha ruwa kenan, wasu kuma asiri ne ake musu hakan ke faruwa, amma Insha Allahu zai basu taimako da ikon Allah cikin zai dawo, tunda ya sha samun cases ɗin nan a kwanakin nan, don haka kawai a mayar da ita gida zai fi." Hakan kuwa aka yi aka mayar da Maryamu gida a cikin wannan halin, ga rashin da suka yi ga kuma fama da ciwon Maryamu Kasancewar an sanar da Iyayenta abun da ke faruwa, ga kuma rasuwar da aka yi, shiyasa suka taho yin musu ta'aziyya, su bakwai suka taho, da Iya Samira da Inna da Umma Jummai, sai Baba da Yaya Faisal da su Yaya Ashiru, a ranan zasu koma su Yaya Naziru, while su Iya Samira zasu ɗan kwana biyu su ga halin da ake ciki Shima a daren aka sallami Hanif ya dawo gida, sai dai jikin nasa babu dad'i tunda a halin da yake ciki na fama da tunani da rashin da aka yi masa, a koyaushe sai dai ka same shi yana hawaye, ya kasa jure rashin da yayi abun ya taɓa shi ba kaɗan ba, kuka yake yi sosai yana mata addu'a a zuciya, har lokacin ya kasa saka wani abu a bakin sa; duk da rarrashin da Iyayensa suke masa, sai dai ruwa da yake jiƙa maƙoshin sa, ƙarshe a gidan su Momy yake kwana tunda bazai iya kwana a gidan shi ba, hakan na tuna masa da mutuwar Amra. While an ci gaba da nema wa Maryamu magani, cikin hukuncin Allah wajen wata biyu kenan da faruwar abun, aka samu ta haihu lafiya a gida, wanda hakan ba ƙaramin farin ciki ya sanya su ba, ta haifi ɗiyarta Mace sak SHAREEF Sai yaran suka zamo tamkar tagwaye da ɗan wurin Hanif, tunda shima yaron sak mahaifinsa ne, yana gidan su Hanif kasancewar ya ƙi yarda a jirga mishi da ɗan, soyayyar da yake yi wa yaron bazai yarda ya kwana a wani waje batare da shi ba, don haka Momy take kula dashi suma suna matuƙar kaunar Yaron, wanda ya ci sunan Mahaifin Amra, wato Abubakar, suna kiransa da Sadiq Saboda wannan sunan da aka saka sai da Sadiq ya zauna ya daɗe a gida bai koma England ba, tunda tun rasuwar shima ya zo, to sai bai tafi ba tunda ya ji an yi masa takwara sunan su ɗaya da Yaron, son duniya sun ɗaura wa Yaron abun tausayi Ga kuma jaririyar Maryamu wacce itama tubarakallah lukuceciya da ita, duk wahalar da ta sha babu abun da ya same ta lafiya lau aka haife ta, sai dai Uwar ce ma da take jinya tunda jikin babu dad'i, Kowa aka faɗa masa haihuwar yayi murna matuƙa, Ƴan Zaria duk sun zo suna ranan suna, yarinyar sunan Amra aka mayar, hakan ya faranta ran kowa. ***** _____  *Bayan wasu lokuta* Izuwa yanzu Hanif ya fauwala wa Allah lamurran sa, yau da gobe yasa ya ɗauki hakuri da dangana ya saka wa ransa, tun yana jin bazai iya manta wa da Amra ba, ga shi yanzu komai ya soma wuce wa ya zama normal, a sanadin haka har ya amince da wasiyyar da Amra ta bar mishi kuma ya ɗauki alkawarin sai ya cika mata, koda kuwa babu son Afra a ransa ne, bare kuma babu yanda za a yi ya ƙi jinin Amra, soyayyar da yake mata yana yi wa kowa nata irin sa, in har jinin Amra ne bazai taɓa ƙyamatar su ba, kuma bare Afra tana kama da Amran sosai, don haka ya nuna ƙudirinsa ya bayyana wa iyayensa wasiyyar da Amra ta bayar Babu wanda yakai su farin ciki gaskiya, musamman yanda suka ga Hanif ɗin; shi da kansa ya kawo zancen, alamun dai yana son ya cika mata wasiyyar ta ne, zasu fi so yayi auren gaskiya a halin da yake ciki yanzu, tunda ga shi lokaci ya ja kusan shekara kenan da rasuwar Amra, kuma sun yaba da tarbiyyar gidan su Amra zasu so su ƙara ƙulla alaƙa; duk da yanzu an zama ɗaya Suma a fannin su Mama babu wata matsalar gaskiya, don a lokacin Afra ta gama secondary school ɗin ta har tayi apply zata shiga nan BUK, kuma Dady da kansa ya biya mata tunda shi ya ɗauki ragamar karatun su yanzu, tuni ya ƙwace ladan a wurin Hanif, tunda ada shi ya soma biya musu, Afra abun ya zo mata a baƙon yanayi, wai Mijin ƴar uwanta yanzu shi ne zai zama Mijinta, abun da bata taɓa tunanin sa ba sai ga shi Allah ya sauya komai, gaskiya baza ta ce ba ta sonsa ba bare biyayyan iyaye kawai zata yi, amma har ranta sai ta ji kamar bata kyauta ba, sai dai kuma Hanif ba irin Mazajen da ake sake da damar samun su bane, ko tana sonshi ko ba ta sonshi baza ta taɓa watsa musu ƙasa a ido ba, bare kuma an ce wasiyyar Yayarta ce, tayi kuka sosai a wannan lokacin da aka faɗa mata, daga ranan sai kuma damuwa ya shige ta koyaushe tana kuka da tuna ƴar uwanta, rashin ta ya dawo mata sabo, Bare da damuwar haɗin auren; wanda ba a fi sati Uku ba aka ɗaura musu aure ta tare a ɗakin auren ta, inda Amra ta zauna Rayuwa kenan! Juyi -juyi, abun da baka taɓa tunani ba sai ka ga shi ya faru, ga Afra da Hanif a matsayin Miji da Mata komai ya sauya A fannin Maryamu ma yanzu komai alhamdulillah za a iya cewa, don lafiya ta samu har ta zana jarabawar ta da kanta yanzu haka ta soma zuwa makaranta Sai ya zamana class ɗin su ɗaya da Afra, tunda itama ana auren ta soma karatun, duk da ba course ɗaya ma suke karanta ba, Yaron Amra ya dawo hannunta sabida Hanif ya ƙi yarda yayi nesa dashi, yana hannun Afra ita take kula dashi, kuma dashi take zuwa school, shiyasa baza ka taɓa cewa ba ita ta haife shi ba, hakan ne yasa Hanif yake matuƙar ji dasu daga ita har Sadiq ɗin Ita kuma Maryamu ƴar iya, ta ƙi yarda ta je da goyo school, don ita cewa tayi, "goyo zai hana ta karatu, yadda take matuƙar ƙaunar karatu bazai yiwu ta haɗa raino da karatu ba." SHAREEF yayi faɗan har ya gaji, haka nan ya ƙyale ta tunda yana son abun da take so, komai take so shi yake mata, don haka shi da kansa yake kula da Yarinyar idan yana gida, idan kuma yana da aiki sai ya kaita school ya wuce da yarinyar wurin Momy, a can zata zauna har sai an tashe su school, sannan zata biya ta can ta ɗauke ta. *ALHAMDULILLAH.... labarina ya zo ƙarshe daga nan da yardan Allah, abun da na faɗa dai-dai Allah ya bamu lada, kuskuren da nayi Allah ya yafe min, Allah ya bamu ikon amfana da abubuwan da na rubuta Amin.* Bazan manta ku ba Masoyana Masoyan wannan littafin, jinjina a gare ku; Nana Aliyu A'isha Yaguda A'ishatu Chindo Zahra Anisa Delicious Soph Fa'iza Fatima Sabo Hafsah Abdul Hafsah Kimba Hauwa Aliyu Hauwa Muhammad Hajiya Maman Khad Jamila Ibrahim Maman Areef Maman Sadik Hauwa el Khabir Murja ce Maman Murja Sani Abu Nafisa Musa Queen Radiya Rahama Ibrahim Ruƙayya Shmciyyer Ummi Zainabu Sister Rukky Fauziya Hafsa Ahmad. Dama wa'danda ban faɗi sunan su ba na fili dana ɓoye, Allah ya bar ƙauna, JIKAR LAWALI na gaishe ku son Fisabilillah 😘 sai mun haɗu a sabon littafina wanda zan sake shi ranan 8/6/2023. *RAYUWAR MADINA!* Ku kasance da Ni don jin dad'i da nishaɗin ku. Please follow me on wattpad UmmuDahira, WhatsApp only 07065334256, Nagode. 2023.