[22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:01 Sadaukarwa ga Sa'adatu Ambassador, Maman Rumaisah, Shafin gabaki daya ta ce , Na gode da karamcin ki tare da gudummawar da kika bawa labarin nan Allah ya saka da alkhairi 😍🌹 _Shimfida_ "Ummina ki min addu'a!" Ya fada cikin matsanancin azaba, hawaye na zuba mata ta ce mishi. "Abu Turab naga gawar Abubakar ban yi kuka ba, na ga gawar Umar ban yi kuka ba, Abu turab me yasa nake kuka akan ka? Me yasa nake kuka???" Mother tears.......! Emir of ilorin palace. 𝗔𝘀𝗮𝗹𝗶𝗻𝘀𝘂 Wadanda suka fara zama a Ilorin su ne Baruba wadanda suka zauna a can tsawon shekaru kuma suka dauki yankin nasu ne; sun tafi ba tare da sanin dalili ba. Sai kuma Ojo Isekuse, wani basaraken Yarabawa, wanda ya zauna kusa da dutsen kaifi inda mafarauta suka taru suna wasa da kayayyakinsu. An yi wa Ilorin suna ne bayan da dutsen kaifi da har yanzu yake wanzuwa. Ana zargin Ojo Isekuse ya fita ne bayan ya yi lalata da ‘yarsa, kuma wani dangi mai suna Asaju ya sauka a kusa da dutsen da ake yankan. Bayan Asaju ne mutane da dama suka zauna a kauyuka masu zaman kansu daban-daban da ke kewayen yankin da ake kira Ilorin a yau. A farkon karni na 19, Ilorin yana arewa maso gabashin daular Oyo, yana da yawan Yarabawa, Hausawa da Fulani. Ya zama hedikwatar wani Janar na Oyo, Afonja, wanda ya kasance sarkin yakin da kujerar Ilorin ce kuma wanda daga baya ya gudu don guje wa yakin kunar bakin wake da aka tura shi ya kashe shi bisa ga umarnin Alaafin na Oyo. Shi kuma wani malamin addinin Islama mai suna Shehu Alimi, wanda ya gudu daga Oyo saboda muzgunawa kungiyar asiri ta Ogboni. Shehu Alimi da Afonja sun kulla kawance domin yakar sojojin Oyo da ke gaba sannan suka fatattaki sojojin Oyo a yakin farko. Alaafin ya yanke shawarar tura wata babbar rundunar da ta tabbata za ta kashe Afonja tawaye tare da kawar da malamin, Shehu Alimi, wanda ya ba da tallafin soji ta hanyar gayyatar Jama’a. Dakarun Jama’a da na Afonja sun kai wani harin ba-ta-kashi a Oyo-Ile, hedkwatar tsohuwar Daular Oyo, inda suka kona ta. Ilorin ya zama babbar siyasa da soja bayan faduwar tsohuwar Oyo. Ba tare da sunan shugaba ba, Afonja da Alimi sun ba da jagoranci ga mutanen da ke zaune a yankin. Afonja da Salih Janta, wanda kuma ake kira Shehu Alimi, sun samu kyakkyawar alaka har zuwa lokacin da Alimi ya rasu a lokacin tsufa. Bayan rasuwar Shehu Alimi, an yi takun-saka da sarautar Ilorin, gari ne mai tasowa. Alfas sun so kafa Halifancin Musulunci bisa ilimi, yayin da Afonja ke shirin sake kafa cikakken mulkinsa, amma Abdulsalam ya fito da taimakon mayakansa. Suna da kwakkwaran iko da Jama'a wanda shi ne mafi yawan sojoji a Ilorin. An kashe Afonja ne a lokacin mulkin Abdulsalam, a lokacin da wata hatsaniya ta barke tsakanin sojojin Yarbawa da Jama’a, wanda ya haifar da matsi na Afonja. An dakatar da addinin Yarbawa da Egungun a Ilorin saboda wannan lamarin. Ilorin ta zama masarautar Khalifancin Sakkwato.[1] Na wani lokaci, Ilorin ta kasance babbar cibiyar cinikin bayi. A da, an fi tura bayi zuwa arewa ta hamadar sahara, amma yanzu ana tura su kudu ta kasashen Yarabawa zuwa bakin teku don samar da bukatu daga Amurka, Indiyawan Yamma, da Brazil. An kwashe bayi daga kasashen Ibo zuwa gabas da kuma garuruwan Yarabawa da aka ci da yaki, da kuma daga yankunan da ke gaba zuwa arewa, ana cinikin tufafi da sauran kayayyaki. Ilorin ya ci gaba da fadada kudu har sai da aka duba shi a cikin 1830s ta ikon girma na Ibadan, jihar Oyo. Sojojin dawakan Ilorin ba su da wani tasiri a cikin dajin da ke kudu, kuma a cikin shekarun 1850 Ibadan ta sami damar samun bindigogi daga ’yan kasuwar Turawa a bakin teku.[1] Kamfanin Royal Niger ne ya mamaye babban birnin kasar a shekarar 1897, sannan kuma aka shigar da filayensa cikin yankin Arewacin Najeriya da Ingila ta yi wa mulkin mallaka a shekarar 1900, duk da cewa masarautar ta ci gaba da gudanar. 𝗗'𝗮𝗸𝘂𝗻𝗮 𝘂𝗸𝘂 𝗱𝗮 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝗴𝗮𝗷𝗶 𝘀𝗮𝗿𝗮𝘂𝘁𝗮𝗿. Saboda irin tarihin da ya ke da shi na musamman na Ilorin, na farko a matsayin Yarbawa daga cikin Daular Oyo, sannan a matsayinta na fulani mai mulkin Halifancin Sakkwato, tana da al’adar yin sarauta wadda ta kasance gauraya da al’adun gargajiya da aka samo daga bangarorin biyu. Duk lokacin da sarautar Masarautar (wadda ke hannun Fulani zuriyar Shehu Alimi) ta kasance babu kowa, wakilin kowace kwata a masarautar wato; Balogun Gambari (Hausa), Balogun Ajikobi (Yarabawa), Balogun Fulani (Fulani) da Balogun Alanamu (Yoruba) - tare da shugaban gidan sarautar Afonja, Mogaji Aare, da kuma babban hakiminsa mai suna Baba. Isale na Ilorin - a taru domin zabar sabon sarki tare da nada sabon sarki, bisa amincewar gwamnan jihar Kwara. Sannan an ba wa Balogun mafi dadewa sarautar Balogun hudu sarautar Balogun Agba, wanda hakan ya sa ya zama na biyu a kan Sarkin Ilorin. Dukkan Balogun na da gundumomi da suke gudanarwa a madadin sarki. Akwai kuma sarakunan gargajiya da kowanne ake kiransa Daudu (ko Hakimin Lardi). Suna aiki ne a matsayin hakimai masu wakiltar sarki a garuruwan dake fadin masarautar Ilorin kamar su Afon, Bode Saadu, Ipaye da Malete, da dai sauransu. Lakabi masu daraja a cikin. 𝗦𝗮𝗿𝗮𝗸𝘂𝗻𝗮𝗻 𝗠𝗮𝘀𝗮𝗿𝗮𝘂𝘁𝗮𝗿 Masu mulki Gyara Sarakunan Masarautar Ilorin:[3] Fara Ƙarshen Mulki 1824 1842 Abdusalami dan Salih Alimi 1842 1860 Shita dan Salih Alimi 1860 1868 Zubayro dan Abdusalami 1868 1891 Shita Aliyu dan Shittu 1891 1896 Moma dan Zubayru 1896 14 Janairu 1914 Sulaymanu dan Aliyu 1915 Nuwamba 1919 Shuaybu Bawa dan Zubayru 17 Fabrairu 1920 Yuni 1959 Abdulkadir dan Shuaybu Bawa 30 Yuni 1959 1992 Zulkarnayni Gambari dan Muhammadu Laofe Dan Bawa "Aiyelabowo V" 1992 Agusta 1995[4] Mallam Aliyu dan Abdulkadir 1995 Zuwa Yau Ibrahim Sulu- Gambari 𝗠𝗮𝘀𝘂 𝗠𝗮𝗸𝗮𝗺𝗶𝗻 𝗺𝗮𝘀𝗮𝗿𝗮𝘂𝘁𝗮𝗿 Masarautar dai ta shaidi irin karramawa ga fitattun ‘ya’yan Masarautar da Sarki na yanzu ya yi. Wadannan sunaye ne da aka ba su;[5] Waziri of Ilorin Emirate Turaki of Ilorin Emirate Zanan of Ilorin Emirate Dan Iyan of Ilorin Emirate Grand Mufti na Masarautar Ilorin Madawaki of Ilorin Malami Ubandoma of Ilorin Emirate Tafida of Ilorin Emirate Shettima of Ilorin Emirate Mutawali of Ilorin Emirate. August -12- 2009 *10:30pm* _Hawaye ne ya zubo mata, sakamakon hango shi da tayi yana wucewa duk da kasancewar dare ne amma hasken da ya haska harabar gidan ya hasko mata shi, yana tafiya cikin ruwa dauke da lema, da alamu ita yake nima. Tirjewa tayi mutumin da ya shake wuyarta ya kuma matseta, tare da jin wani bakon al'amari yana ratsa jikinta, cikin tsannanin azaba da masifar da bata tab'a haduwa da shi ba. Wani irin ajiyar zuciya take saukewa, tana jin kamar ta mutu ta huta. Haka ya gama keta alfarmarta sannan ya tashi a kanta, duk da bata ga fuskar shi ba, sai dai kamshin turaren shi ya tabbatar mata da waye a tare da ita. A hankali ta yunkura zata mike suka sake mai da ita, haka su hudu nan suka keta alfarmarta. Kafin daga bisani suka shake ta, sai da suka ga bata motsi sannan suka kyale ta_ ****************************************** Sokoto State... Binji LG Maikulki Rabewa gefe tayi, ta dauki kokonta ta koma can jikin bango ta tsuguna tana sha hawaye na zuba mata. D'ago fararren idanunta tayi tana kallon Mahaifin su da ya shigo. Yana kallon tsakar gidan, "wallahi duk lokacin da na kalli Sa'adatu sai naji kunya ta kama ni, musamman idan ta fita cikin mutane ana nuna mu. Duk sai naji na muzanta. Shi yasa bana kaunar tana fita da shegen idanunta a wurin." Ya fada yana tsaki. "Larai zuba min abin karyawan nan, kuma ki tabbatar sun shirya su tafi makarantar idan Allah ya jarabce ka da haihuwar bakar ƙaddara babu yadda ka iya, yanzu don Allah taya zata fahimci karatu." Tab'e baki yayi yana kallon matar da ta fito daga madafin. Duban inda yarinyar take tayi na dan lokaci kafin ta ce mishi. "Bawa baya tab'a kaucewa ƙaddaran sa, Malam itama ba sayawa kanta tayi ba, duk da haka ba zai saka mu tsane ta." Ta fada tana wuce shi. Tsaki yayi yana faɗin."haka kawai an tashi an haifa min nakasashiya a cikin Yarana." "Sai ka gayawa Ubangijin da ya baka ita ka ji" ta bashi amsa, daukar ƙara yayi nufi Yarinyar. Ganin shi dauke da kara yasa ta sake kofin kunun hannunta, ta mike zare mata idanu yayi cikin masifa ya kira Yan uwanta. "Harirah, Rabi" fitowa suka yi sanye da Uniform, fari da hijab din su iya cinya. "Na'am Baffa" "ku bata kayanta itama ta biku tunda abin na munafunci ne ta tafi tunda na san ba gane kome zata tab'a yi ba." "Wai Malam meye Sa'a ta maka ne? Makarantar nan dai wallahi ko kana so ko baka so dole ta je" "Assalamu alaikum, iyyi lafiya?" "Yaya wa'alaikumunsalam sallama, Alhamdulillahi gara da kika dawo wallahi na rasa yadda zan yi da Malam akan Sa'a " kallon shi matar tayi,.kana ganin fuskarta kasan ranta yayi azababben ba'ci." Gyada kai tayi sannan ta nufi wurin Yarinyar me suna Sa'adatu" "Tashi ki shirya yanzu na saka hansiya ta dinka miki kayan ki." Murmushi tayi tana share hawayen ta." "Innah laminde zamu makara fa" "kuje zan kawo ta" "ba da yawuna ba zaki fita na dai gaya miki" Malam ya fada yana kad'a babban rigar shi. Juyawa tayi ta ce mishi, idan kaga ban fita ba, tow bana numfashi shi ne fita ya zama wajibi ne" ta riko hannun Sa'a ta kaita banɗaki ta wanke mata jiki, zasu fita ta riko hannunta. Ta kanne mata ido daya, tare da mata alamar ta mata wanka kawai don Allah. Murmushi tayi tana faɗin."Sa'ade zaki makara dai" hakan ta kuma dibo ruwa ta mata wanka tass. Sannan ta fito da ita shirya ta tayi, ta dauko mayafinta tana faɗin. "Larai bari na kai Sa'a makarantar." "Tow Yaya sai kin dawo" bata ga malam a cikin gidan ba, alamar yana kofar gida, koda ta fita ta same shi tare da mazan makotar su. Haka ta wuce su, bata mishi magana ba. "Aminu idan Sa'ade ta kara girma ka aurar da ita mana tunda kaga ita Uwarta bata san harkan arziki ba." Kallon mutumin yayi kafin ya ce. "Ilya babu me auren Sa'adatu, duk da ni kaina nasan duk cikin Yarana babu me kyanta kuma ba za a kuma samu ba, sai dai ina jin takaicin haihuwar ta da aka yi a gidana babban kuskure na, shine gaya mata Yarinyar zata tafi kurmi niman kudi gashi abin haushi daya yadda Uwar lamaran ta kwadaita min arzikin da suke samu. " Shiru suka yi kafin Malam Musa ya ce mishi. "Kuma kaga kuma Laminde bata kyauta ba, ai bai dace ta kai ka gidan me gari ba domin dai nasan idan kuka samu arzikin nan tare zaku ci shi,ba kai daya ba waye ya sani ko har da Hajji zaku tafi." Kwafa. Malam Aminu yayi yana faɗin"Yo shima me garin ai bakin munafiki ne, ina cewa kin min magana yayi sai ganin dogarai kawai bisa kaina, wai daga gidan Hakimin Binji" kwafa ya kuma yana kallon hanyar da suka bi, yana tuna irin cin zarafin da aka mishi, anan yaji wani yana cewa za a kara musu malaman makaranta. "Tass mai gari ya ci zarafina, da goyan bayan hakimi, duk amanar da yake tsakanin mu na tsawon shekaru wai don Laminde ta kai ƙarata akan nakasassshiyar yarta ya zauna ya tsefe ni kamar ya samu kitso har da cewa bani da imani. Waye zai yarda a haifa mishi nakasashe kuma abin takaici nifa ban hanata kome ba, Bara kawai zata tayi mu samu kayan alatu amma uwar ta hana mu na dai san da ace ta tafi meye ba zamu samu ba? ?" "kai Malam Aminu ka ji tsoron Allah bayan haihuwar ta tasamu ciwon ba haifarta kuka yi da shi ba." "Eh meye maraban dambe da fada? Gaya min meye bambancin? An haife ta da shi ko ta samu ai duk daya ne, babu abin da ya min ciwo kamar kashe kudina da nayi na bin hawa, sannan itama Laminde aka saka ni na biya mata, Allah ya isa min" ya fada kamar zai yi kuka. .... Inna Laminde har kofar aji ta raka Sa'ade. Sannan ta leka ajin, "Malam ayi hakuri ta makara " "Ba kome innah " "mun gode sosai" sannan ta nuna mata cikin ajin, rike yar jakar buhun simintin ta tayi me littafi kwaya uku. Zama tayi Innar ta leke ta, tare da d'aga mata hannu. Bata fuska tayi kamar zata yi kuka. Domin rashin yarda irin na Sa'ade. Murmushi Inna tayi ta bar makarantar. A hankali taji hawaye ya zubo mata, tausayin rayuwar Sa'a take, tayi kankanta da fuskarta al'amari me girma haka. Sai dai kamar yadda Uwani matar me gari ta gaya mata dole ita zata tsayawa Sa'a.. Asalin su yan garin Maikulki ne, ko nace mazauna garin. Fulani ne da suka fito daga yankin sahara, domin yanayin su ya fi kamancecceniya da bororoji. Sai dai su fararren ne, ba bakaken fulani ba. Duk da suna yawo ne da dabobbi kafin su zauna a garin Maikulki na karamar hukumar Binji, Garin... [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Dedicated to Handicapped ❣️😓 ```Ina mata yan kamshi matan yan yayi TOH ga turaren mu nan. Ga turaren orientica kuzo kusiya arha kwasha kwasha 1700``` Page:02 Gari ne mai cike da albarka, lokacin da suka zo garin tana amarya kusan shekaru arba'in kenan. Tana da yara shida da Malam Aminu, uku maza maza uku mata. Haka abokiyar zaman ta, Larai tana da yara biyar. Ƴaran Inna Laminde sune manya akwai Zakari ya'u, suna kiran shi Ya'u sai Yusuf suna kiran shi Dabo,sai Ibrahim suna kiran shi Iro, sai Alaweeyah suna kiran Addah Weeyah sai Shamsiyah tana kiran Maman Sailuba, sai Auta wacce haihuwar yazo mata a bazata domin a tunanin su tun kan Shamsiyah don sai da ta girma sosai domin takai shekaru goma aka haifi Auta Sa'ade. Ya'u yana zaune a Sokoto shi da iyalin shi, domin da taimakon Allah da samun jajjurtaciyar Uwa Ya'u ya samu ilimin boko, na Addini kan dama suna yi. Na bokon ne Malam Aminu yaki cire kwandalar shi su amfana da shi. Fadin irin wahalar da Inna Laminde ta sha akan Yaran ta sai Allah, domin har surfe sai da tayi ita burinta Yaranta su samu ilimin. Alhamdulillahi Ubangiji ya dafa mata domin bayan Ya'u ya samu diploma akan aikin jarida, wata gidan Radio a sokoto ta dauke shi aiki, dama Yusuf yana na shi karatun domin shi jami'an danfodiyo ya samu, inda yake bangaren kimiyya kere-kere. Iro kuwa kasuwanci ya faɗa, domin yaki bokon tunda ya gama secondary ya ajiye boko, sai Allah ya saka mishi albarka shi kan yana garin Binji a can yake kasuwancin shi. Wani ikon Allah yaran duk sun san wahalar da Uwar su ta sha, haka yasa basu da wacce suka sani sai ita. Ɗakinta kuwa da ita kanta da suturan da take sakawa wallahi zaka dauka wata hamshakiya ce, nan kuwa ba kowa bace. Duk karshen wata suna hanyar me kulki dukkan su kuwa. Haka yana mugun yiwa Malam Aminu ciwo duk da ya hana su, moran shi amma Yaran basu mishi kugunta ba. A kome sukawa Mahaifiyar su zasu mishi, shima albarkacinta yake ci. Ba karamin al'amari ba ne domin lokacin da suka ce su boko zasu yi ba zasu yi kiwo ba, cewa yayi sai dai tana fita mishi da kiwo. Haka ta amince dake tana da wata kawa matar mai gari ita ta bata Shawaran ta saka Yaranta a makarantar boko, babu amfanin barin su suna yawo a daji da sunan kiwo. Ita kuwa ta amince. Shine fa aka fara samun matsala da Malam Aminu. Har aka haifi Sa'ade yarinyar ta taso cikin kulawa da soyayyar yan uwanta. Musamman Addah Weeyah da ta kusan aure. Domin itama tayi karatu har zuwa aji uku na secondary su, kafin Uban ya daka tsalle ya ce bai iya ji ba, duk da kiri-kiri yake fifita yaran Larai akan Yaran Inna Laminde. Yaran Larai sun, Yakubu, sai Jamilu, Ikilima tana aure, sai Harirah da Rabi. Ikilima tana aure a Binji gidan Sarkin Fulani. Domin Larai Mahaifiyar ta yar gidan ce, Malam Aminu kyakyawan gaske ne, idan ka gan shi ba zaka tab'a yarda shi ya tara Yara har goma sha daya haka ba. Haka itama Innna Laminde tana da kyau na asalin Fulanin Somalia. Laluran Sa'ade ya faru ne sakamakon cutar bakon dauro da aka yi, wanda kowa yasan yadda ciwon yake,. Shi ya tab'a mata wuyarta da kunnen ta daya. Bata ji da kunne daya sannan bata magana. Domin tana da shekaru biyar ciwon ya same ta, da farko har an fasa kukan ta mutu, sai da aka zo mata wanka sai a ka ga tana da sauran numfashi. Haka ta sha jinya kafin Allah ya bata lafiya. Sai dai fa bata hmm-bata humm- haka laluran ya same ta. Yayunta har asibitin Udut suka kawo ta, amma ba baki ba ido a lokacin karfi imani ne kawai yasa Inna Laminde bata mata fatan ta mutu kowa ya huta ba. Gashi a lokacin bata isa ta fita wasa ba, idan yara suka mata magana suka ga bata amsa ba, sai su watse su barta. Idan tana jin wuyan haka zata zauna tayi ta kallon uwar hawaye na zuba mata, sai taga kwano zata dauka tana budewa. Akwai lokacin da Inna Laminde ta tafi zaman bikin Ikilima da ta haihu, Yarinyar nan ta sha wahala domin ba kowa ke gane abin da take so ba, dama idan Innarta tana nan kwanciya take a jikinta ta hakan take fahimtar bata da lafiya. Sai kuma idan tana jin yunwa zata yi ta buɗe kwanika tana kuka. Tow tunda uwar ta tafi dake tana da kulafuci, don ta Uwar ce tare zasu tafi malam ya hana wai zata ja mishi magana a ce gidan shi a kwai kurma. Haka ta tafi tabarta cikin jinya domin bata da lafiya sosai, ita kuwa Inna Larai bata sani ba, sai da ta kwana bata ga tazo taci abinci ba, shi ne da safe ta leka dakin nan ta ganta a gadon bunun Innarta, yadda ta d'aga labulen dakin ta bude idanunta da suka yi jajjur, tana kallon ta kafin hawaye ya zubo mata. "Ni Maimunari yarinyar nan Allah yasa ba wani abu ke damunki ba" ta shiga ta tab'a kanta, jin yadda ya dauki zafi yasa ta fitowa ya cewa Malam da yake zaune a tsakar gida. "Malam taimaka ka bani cafeno yarinyar nan bata da lafiya, jikinta yayi zafi sosai." "Ke Larai bana son munafunci, ta mutu mana ko an gaya miki ina mara ba ita ne gara ta mutu kowa ya huta." Shiga ɗakinta tayi ta bankade zanin gadonta ta dauki kudi, ta fita yana mata magana amma ta bawa banza ajiyar shi yaji haushi kuwa, haka ya shiga dakin da tsumagiya ya shiga zane Sa'ade. Ga ciwo ga duka, Allah ya gani ya tseneta kamar ya kashe ta, yana cikin dukarta Inna Larai ta shigo gidan. Dakin ta nufa da ta ga takalmin shi. Ganin yadda yake dukar ta yasa fasa ihu, don ta suma. Fada sosai suka yi da Malam ta maida Sa'ade ɗakinta domin Rabi da Harirah sun bi Inna Laminde sunan Ikilima. Fadar irin kiyayyar da Malam yake nunawa Sa'ade sai ya baka mamaki. Haka ta taso da mugun tsoron shi, tana ganin yadda yake dariya da farincikin da yan uwanta amma ban da ita. Lokacin da ta cika shekaru tara Ya'u da Yusuf sun tsayar da shawarar su tafi da ita wurin su, amma bawan Allah nan fir yaki kuma ya hana a sakata a makarantar. Haka suka hakura itama bata son nisa da Innarta. Ana haka wata mata da take zuwa sayan madara a gidan ta jima bata zo ba. Dama bata da aiki sai daukar yara tana kaisu birni aikatu, masu laluran kuma tana kai su irin su Abuja da Lagos bara. Haka yasa ta wannan zuwan da zata koma an bata sakon madara zata saya shi ne ta ga Sa'ade, shi ne ta tuna akwai wani me kudi a can Lagos da ya ce ta nima mishi kurma mace ko namiji zai dauki nauyin a mishi jinya. Ganin Sa'ade yasa abin da take hangowa zata samu ya kara rikita mata lissafi, tasan Malam Aminta da mugun son abin duniya, don haka tana gama amsar madaran ta dauki kuɗi me yawa ta bashi kudin madaran sannan ta bawa Sa'ade kudi me yawa tana faɗin. "Malam Aminu ga arzikn a cikin gidan ka, amma ka kasa amfana da shi, gaskiya ya kamata ka san darajar haka." Ta fada tana kallon Sa'ade. "Kina nufi wannan abin Arziki ne? Hhhhh" ya fashe da dariya, yana nuna Sa'ade da take zare idanu. Domin tasan duk lokacin da Baffan su ya nuna ta yana magana tow ba abin dadi yake fada akan ta ba. Mikewa tayi daga bawa dan ragon ta madara a fidinbotul,ta koma dakin Innar su. Da take kallon kofar dakin. Kallon juna suka yi ta koma bayan Inna Laminde ta kifa kanta tana sauke ajiyar zuciya, hawaye ne masu zafi suka zubo mata, tana matukar tausayin yarinyar da bata ji ba bata gani ba. Malam Aminu suka fita da Tabawa, anan ta tsara shi da kudin da zai samu, akan Sa'ade, ta mishi alkawarin wani sati zata zo in sha Allah. Bai fadawa Inna Laminde ba, kawai yayi gaban kan shi. Sati na zagayowa kuwa sai gata da uban kudi dama tun ana gobe zata zo, ya ke cewa Inna Laminde ta shirya Sa'ade gobe tabawa zata zo ta tafi da ita. Aikuwa tace bata san zancen ba, duk abin da za ayi sai ayi. Yarinya shekara tara ya hana a saka a makaranta sannan ya ce za a kaita wani wuri. Haka suka kwana suna rigima, washi gari sai ga Tabawa ta zo, ganin da gaske rabata zasu yi da Yarta. Don haka bata yi kasa a gwiwa ba, ta dauki yarinyar suka nufi gidan Mai gari, tun safe ake babu ɗaya shi kuwa ya kafe sai an tafi da Sa'ade, Mai gari ganin al'amarin yafi karfin shi yasa su a gaba har zuwa gidan Hakimi. Anan aka yi ta ta kare, har yake barazanar sake ta, dake suna shiga garin Binji ta samu wani Yaro a gidan Hakimi ta tura shi ya kira mata Ibrahim, can sai gashi a gaban shi aka yi Shari'ar inda Hakimi yasa a bincika mishi Makarantar Maikulki ko akwai malamai, nan me gari ya gaya mishi babu wasu malamai ba sai an kai da bincike ba, a duba kodan rayuwar Sa'ade. "Zan yi magana da shugaban karamar hukumar Binji zai yi magana Baturen ilimi in sha Allah za a kawo ma'aikata da yarda Allah, ita kuma Sa'adatu Mai gari idanun ka ya tsaya akan ta, sannan duk abin da yake tafiya zan na tuntubar ka." "In sha Allah zan saka Idanu " "kai kuma wallahi naji labarin wani abu ya kuma faruwa sai na tura sakon zuwa shugaban ƙaramar ƙungiyar kare hakkin dan Adam sun daure ka. Kuma itama Tabawa a gaya mata ta bar kasar Binji kafin na same ta." Da wannan aka kashe zancen, Allah da ikon shi ya hadata da matan me gari, tayi ta bata shawara. Yadda zata kula da Sa'ade. Koda suka dawo gidan ma tashin hankali da masifa, dama shi Ibrahim tun a can ya bawa Babar su hakuri domin yasan halin Baban su, ba zai iya rigima ba. Haka ya tasata a gaba da bakar magana kamar zai doke ta. Laminde ke nan, a yayinda takwarorinta suke kurmi da kudu niman abin Arziki shi ne zaki tozarta ni ta hanyar kai kara na, gidan Anamimin can wato ki jindadin ayi min dariya tow na gode tunda a iya gidan hakimin Binji kika tsaya na zata zaki wuce har lahira ne da ni. Karewar Gidan hakimi, tow wallahi na rantse da Allah babu hannuna a kan Yarki ku nima mata wani Uban ba ni ba." Haka gefe guda Abokan shi zuga shi suke akan Laminde tafi ƙarfin shi ashe kuri yake da karyan yafi karfin gidan shi. Ita kan Inna Larai babu ruwanta domin har ita bai kyale ba, shi yasa bat shiga cikin hayaniyar su. --- a dawo labari. Federal Ministry of education Sokoto State Kamar yadda Hakimi ya tura sakon shi, haka Shugaban karamar hukumar Binji ya tura zuwa ga Commissioner ilimi. Dr Sharif Hamidu. Kasancewar yau satin shi biyu da dawowa daga Umra. Ya kuma yi daidai da kwanakin da ya ɗauka na Hutu. "Yallabai akwai takardun da aka turo da kuma na aiki, daya daga karamar hukumar Binji. Kwantomar Binji da kan shi ya kawo yana bukatar a baka sakon" kallon sakataren shi yayi kafin ya ce. "Ok na ga ni" mika mishi takardan yayi, ya duba kafin ya zuba mishi idanu. "Suna bukatar malaman makaranta ne." "Tow ko za a tura wurin me girma Gwamna ne" girgiza kai yayi sannan ya ce. "A tura musu yan bautar kasan da za su yi service makarantun mu, sannan zan tuntubi me girma Gwamna da maganar." "In sha Allah za ayi haka." "Allah ya sa" ya furta, Fita sakataren yayi shi kuma ya fara aikin shi da ya bari. Yana nazarin maganar da shugaban karamar hukumar ya turo mishi. Akwai yara masu yawan gaske da suke buƙatar kulawar Malami da gwamnati, a halin da ake ciki har an fara diban yaran nan zuwa birane domin niman kudi wasu Bara, da sauran su. Babban abin damuwar yarinyar da ake son a fita da ita bata ji bata magana kuma a haka za a fita da ita birni ba a san inda za a tsaya da ita ba. Cire glass din shi yayi yana mamakin wannan al'amarin. Me ya dace su? Dole a tura musu malaman, wayar shi ya janyo ya gwada kiran me girma Gwamna... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:03 Kiran wayar yayi bai shiga, iskar bakin shi ya furza, sannan ya cigaba da aikin gaban shi. Yana kara nazarin yadda zai ɓullo al'amarin. Domin yana son lallai a tura malamai da yan bautar ƙasa kananun hukomammin da ƙauyukan da suke cikin su. Haka ya zauna yayi dogon rubutu zuwa mai girma gwamna, ^^°°•• Kan wuri unguwar Sarki. Fadar Sarkin Musulmi. Alhaji Shehu Abubakar Shehu, shi ne mai martaba sarkin Musulmai, sarki na goma sha shida, Allah ya albarkace shi da nisan kwana tare da iyali masu yawan gaske, daga cikin yaran shi akwai manyan mutane kuma jami'in gwamnati da sauran su. Kananun yaran shi sune waɗanda suka gama secondary, yan mata biyu. Yayun su maza sun gama jami'a suna bautar ƙasa. ... Bangaren shi kan sa mai Martaba, babban sashi ne me cikin gashin kan sa. Zaune yake a falon shi hannun shi rike da tangaraho, yana amsa magana da ita. "Kuma kun bincika kome? Yana da kyau kafin ka zartas da hukuncin ka fara bincike, ban ga kome a tattare da shi ba, sai gaskiyar shi da nagartar shi. Karka manta mugu ko mutumin banza baya zuwa inda nake, kai ko laifi yayi ba zai tab'a zuwa inda nake ba, balle har ya samu damar zama a cikin gidan nan ka sake tunani kar ka lalata alaƙar ka da d'an ka domin wani abin da baka da sanin faruwan shi." Sun jima suna magana kafin ya katse wayar da addu'a. Kallon Hajiya Umma yayi uwargidan sa, mace me nutsuwa da kamala. Ga hakuri da juriya hadi da kawaici me yawan gaske. Kowacce mace da tazo gidan bayan ta ce, babu macen da ta sha wahala da Mai Martaba Shehu Abubakar Shehu irin ta, domin auren su na hadi ne, tasha azaba da zilla. Shi yasa har kwanan gobe shi da kansa yake jin kunyar kallonta, domin akwai wani abin da ya mata har yau tabon yana kan fuskar ta. "Ummul Hafsah." Ya kira sunan ta a hankali, yana kallonta. Yadda ta tattaro nutsuwar ta akan shi, yana daga cikin abin da yake kara kashe shi a kaunar ta, yadda duk yadda ya kirata tow zaka samu tattara kome ta ajiye ta mai da shi sama da abin. Riko hannunta yayi cikin na shi, a kalla auren su zai kai shekaru hamsin da wani abu. Yadda take kallon shi ya saka mishi wani irin nutsuwa. "Ina jin ka mai Martaba" ajiyar zuciya ya sauke yana gyada mata kai. "Ummul Hafsah! Misali Muhammad Rabi'u aka zarge shi da laifi me zaki yi akan shi?" "Ban fahimci abin da kake nufi ba?" "Ina nufin Muhammad Rabi'u a zarge shi da kisan kai me zaki iya yi dan wanke shi?" Rike hannun shi tayi tana kallon shi. "Zan hana idanu na barci na gayawa Allah matsalata, sannan na nemi taimakon shi ya fitar da gaskiya." "A matsayin ki na uwa me zaki yi bayan haka?" Ya kuma wurga mata tambayar da yasa ta kura mishi Idanu. "Ba zan gushe ba sai na tabbatar da cikakken gaskiya ta hanyar binciko me laifin , sai dai idan an fi karfina na zuba idanu na cigaba da gayawa Allah halin da muke ciki " matse hannunta yayi a hankali sannan ya cigaba da cewa. " Halin da Yaron nan yake ciki kenan Allah ya kubutar shi" "wani Yaro kenan? Ba dai dan Badi'atul Noor ba?" Ta tambaye shi jikinta yana rawa. Murmushin karfin hali yayi ya riko hannunta. "Ita Ummul Hafsah" janyota yayi jikin shi. "Kar ki karaya, kar ki bari Yaran su san halin da ake ciki domin zai iya shafar kwanciyar hankalin su da shi kan sa Yaron don Allah ki manta abu me muhimmanci yazo yi isa aka d'aga mishi hankali ba zai yi ba, sannan tun daren jiya Badi'atul Noor ta kira ni, ta gaya min halin da take ciki da matsalar da take kai. Sai yau Abdulrahman ya kira ni shima ya gaya min bana son a kai ga Yaron ya sani. " Cikin sheshekar kuka ta ce "tow in sha Allah " amma tsakani da Allah ta kad'u domin sanin da tayiwa Badi'atul Noor akan Yaranta bata wasa a kan tarbiyyar su, musamman wannan da ake zancen akan shi. Kasancewar safiya ce kuma lokaci ne na zafi sosai. Ila kowa yasan yadda ake zafi a Sokoto. Sanye yake da sport wear. Sai facing cap, ƙafan shi sanye da takalmin kamfanin Fila. Gefen shi Yarima Sadeeq Autan Ummul Hafsah, a hankali suka fito shi Yarima Sadeeq yana kan keke shi kuma yana tafiya da kafar shi wato yana jogging. Haka suka tafi garin babu wani cunkoson mutane. Haka suka yi ta tafiya, "A.A baka kira gida ba ne?" Murmushi yayi yana cigaba da tafiyar shi har suka isa inda zasu motsa jikin. Wayar shi ya ciro ya gwada kiran Number gida har ya karaci ringing babu wanda ya dauka. Kamar ba zai magana ba, ya d'ago kai ya Kalli Sadeeq cikin sanyin murya sanan ya ce mishi. "Na kira basu dauka ba." "Amma kuma lafiya dai?" Shiru yayi yana kallon wasu matasa biyu yadda daya yake rike da hannun dan uwansa suna tafiya a hankali. Janye idanun shi yayi daga kan su, ya mai da hankali shi kan Yarima Sadeeq. "Wani abu ka ce?" Murmushi yayi yana faɗin "hankalin ka yana wani wurin ina zaka fahimce ni, mu karasa abin yake gaban mu " Haka suka gama yar tsalle tsallen su sannan suka wuce gida, wanka suka tare da shiryawa cikin shigar kayan bautar ƙasa, suka nufi sashin Hajiya Ummul Hafsah. Anan suka karya tana jan su da hira. Shigowan wasu yan mata biyu, suka nufi Ummul Hafsah suka gaida ta, sannan suka Juyawa kan su Sadeeq da A.A suka gaida shi. "Wadannan Kannen na ne, ita wancan sunan Nimrah sai wannan Amirah Yaran Amryan Mai Martaba ne" Sadeeq ya fada mishi haka, gyada kai yayi sannan ya mai da idanun shi kan Ummul Hafsah ya ce mata. "Ko kin yi magana da Ummina? Ina ta kiran su tun ranar da nazo ban same su ba, idan ya shiga basu dauka don Allah ki kira min ita mana" yayi maganar kamar zai rusa ihu, tabbas ya sakankance dayawa duk da yana da Yayu manyan kuma maza waɗanda basu zaman kasar baki daya, amma shi har yau kamar Baby ne a wurin Ummin shi, kasancewar shi Auta da Ummin shi take masifar kaunar shi. Wani irin kauna ce me zafi tsakanin shi da Mahaifayar su. Yadda ya tsare ta da idanu yasa babu shiri ta janyo wayar ta, Blackberry cobbler, ta kira layin ta. Sai da ya gama ringing sannan ta yanke. Sake gwadawa tayi ai kuwa ta dauka. "Sultanah Badi'atul Noor!" Da sauri ya sauka akan kujeran cin abincin ya koma gabanta kamar zai shige jikinta. "Baba karami yake son magana dake" "Ki bashi" mika mishi wayar tayi. "Ummina me yasa Ummul Mansurah bata daukar wayata? Ummina har sako na tura mata bata dauka ba, please Ummina ki taimaka min ta min reply" "hmm bata nan ne kuma na amshe wayar." "But why?" Yayi maganar a shagwab'e yadda zaka fahimci shi din Babyn Ummin shi ne, zaka iya rantsewa da Allah a gabanta yake, domin yadda yake narkewa like zai shiga cikin wayar ita kuwa a can wani irin tausayi yake bata. "Ummina rabona da ita yau kwana biyu fa" "ban ji me kace ba?" Ta tambaye shi a hankali, "Ummina ina ranar da ta turo min sako na tawo part din Grandma nazo na dauke ta? Tow rabona da ita ke nan" "na tuna shi kenan " ta ce mishi, "Ummina don Allah ki ce ta turo min da sako ina jiran ta" abin ya bawa Sadeeq da Ummul Hafsah mamaki, ashe dama haka yake da magana, baki daya ya koma kamar me cutar hakori. Haka suka fita. Sadeeq ya kalle shi, sannan ya fashe da dariya. "Dama haka kake Prince? Na zata duk wannan kamewar da rashin walwala duk cikin jinin sarauta ne" bai tsammaci zai amsa ko yayi wani babu ba sai gashi ta fashe da dariya shima, cikin walwala da farin ciki ya ce. "Ummina da Dad, Ya Abubakar, Ya Umar, Aunty Zakiyyah, Aunty Rumaisah, sai Gran princess Ummu Mansurah, sune farin cikina, bani da wasu bayan su, mulki ko isa, kasaita ko d'agawa basu cikin abin da yake gabana. Ni free Man ne, ina son Freedom, ko rashin maganar da kuke gani bana yi rashin sabo ne. But tunda nasan Ummina da Ummanku, yan uwa ne sosai naji zan iya spending rayuwata a sokoto ka fahimta?" Ya fada yana zuba hannun shi a cikin aljuhun wandonsa yana me d'aga kafad'ar shi. Yayi wani kitty face. Irin fuskar mage nan. •••°° Maikulki. "Malam Aminu, shin baka ji labarin tallafin da gwamnatin tarayya take bawa nakasasu ba? Jiya ina jin labaran BBC Hausa, naji an kawo tallafin nan Sokoto, a madadin makarantar da zaka kaita me zai hana ka shirya ta ku tafi birni a baka taimako kai ne baka sani ba, amma Arziki ne a cikin gidanka fa. " Shiru yayi yana kallon Malam Musa, kafin ya ce "eh tow zan yi haka, amma yanzu kaga yau juma'a tana zuwa Binji wurin yayanta, idan na ce zan yi wani abu Laminde da wancan Annaminin zasu yi magana zan bari sai ranar sati Laraba sai na nime sa'a," "yawwa kaga kasami hanyar kutsawa da ita niman taimakon za a mata aikin kunne da baki kafin ace me ka tara kudi sai ka tashi gini ka auro bazawaran nan, tunda ba zaka iya sayar da shanuwarka ba" "kai Malam Kalla Ubangiji ya biya." "Kar ka damu zaman tare yafi karfin haka, dole na tsayawa abokina irin ka, ga arzikn har akwai macen da zata maka bakin ciki da shi? Bata isa ba wallahi sai mun mori kayan mu ka kwantar da hankalin ka, an yi an gama yarinya takace kuma dole ka mori nakasar ta haka kawai za a ce baka isa ba. Inji Uban waye?" "Bari naje gidan ma wannan yarinya ba karamin takaici nake ji ba, amma yanzu da nasan zanci moriyar ta zan rage takaicina akan nakasarta. Haka ya baro gindin maina yana ayyana yadda zai tafi Sokoto da Sa'ade. ..... Yau ma sai da aka mata wanka domin shegen tsaftar da Allah ya daura mata, shafa mata man gyatuma radau Inna Laminde tayi hannu da kafa, sai ta fito shar amma abin ka da wanda ba a iya mishi sake daukar man tayi, ta shiga shafawa a jikin ta zaka rantse da fadawa cikin mai, musamman yadda tayi naso. D'aga labulen dakin Malam Aminu yayi ta sake roban tayi a rikice, tana zare idanu waje. "Yar banza me kama da mayu." Ya fada yana shiga dakin, dukar da kai tayi kasa tana kallon yadda hawayenta yake d'iga. Wani irin lafiyayyen rankwashi ya sakar mata wanda yasa ta zaman dirshan. Tana sosa kanta, sake zuba mata rankwashin yayi fitsari ya kwace mata, "shegiya ba yau naso ki mutu ba, da na kyale ki shi ne ba zaki taya ni ni man arziki ba, ba banza Allah ya barki baki magana baki ji da kunn..." "Allahu Akbar! Ashe haka kake malam? Kashe min Y'a zaka yi? Me Bimbi ta maka? Meye ta tsare maka?" Juyawa yayi cikin borin kunya ya kalle ta yana inda-inda. "Yarinyar nan sai da nace miki matsiyaciya kika haifa amma fir kika ki ganewa, so nayi tuntuni ta mutu amma kika ki gata nan tana min kafar angulu, ita bata rayu cikin Mutane masu hikima da lafiya ba, gashi ta rayu cikin nakasasu taya zan ji farin cikin ganinta shegiya munafuka wallahi na gaji da ganin ta, Anya kuwa jini na ce ita?" Zaro idanu Inna Laminde tayi tana dafe kirjin ta. "Innalilahi wa'inna laihil raju'un Ubangiji ka hana kunne na jin mugun ji da mugun gani Malam karka sheganta min Y'a mana, ba ita tayi kanta ba malam" ta fada kuka yana kwace mata. "Tow wallahi idan har kina son na amince da ganinta a matsayin jini na ki cire hannunki akanta" "wacce irin rayuwa ce haka Malam? Gaskiya ba zan iya ba" "tow wallahi tayi ta ganin ukubar rayuwa kenan. Domin ba zata tab'a ganin farincikin a cikin gidan nan ba" ya saka kai ya fice a dakin yana mita. Zama tayi a bakin gadon tana kuka, daga ita har Sa'ade babu me bawa wani hakuri. Tashi tayi tana goge hawayenta, ta dauki kayan Makarantar ta, ta saka sannan ta saka hijab ɗinta, da jakar buhun simintin ta fito tana tafiya a hankali kamar wacce kwai ya fashe mata. Har ta fito gida kanta a sunkuye yake, bata yarda ta kalli sama ba, domin a tunanin ta Baffan su yana kallon ta, kuma zai iya make ta, Allah ya zuba mata masifar tsoron shi, domin wallahi gara mutuwa bata gan shi ba, amma Baffan su tana mishi kallon mutuwa ne baki ɗaya. Shi yasa matukar yana gida baka tab'a ganin ta a cikin yara ko a kofar gidan, domin hantar da yake mata ga duka kamar ba shi ya haife ta ba. Haka ta isa makarantar dake su harirah da Rabi sun tafi. Tana isa ta wuce ajin su. Abin da yake damunta, bata fahimtar kome gashi nan a rubuce a bango amma bata san me ake nufi ba, haka yasa baki daya bata da wani walwla da kuzari. Ko da aka yi break tana zaune a saman window din ajin tana kallon Yara. Sai sha'awa suke bata. Amma da zata tafi cikin su yanzu zasu watse haka yasa take kallon su daga nesa. Har aka koma Aji ta koma wurin zaman ta. Wasu yan mata ne suka zo inda take suka shiga mata dariya. Kanta kawai ta kawar idanunta yana cika da kwalla. Domin idan akwai abin da ta tsana ta ga Yara suna mata shakiyanci. Haka yasa bata cika son shiga cikin su ba. Sai da malamin social studies ya shigo yaran suka koma wurin zaman su. Ire-iren matsalolin da take fuskanta kenan ko a gida ko a makarantar su. Haka yasa ta fara kokarin kin zuwa makarantar idan aka tashi kuka take sakawa Inna Laminde ita ba zata ba. Zuba mata idanu tayi yau da ya kasance Juma'a. Duk da wankar da Inna Laminde tayi mata da wuri, wai kada ta makara, bai hana ta komawa saman gado me rumfar Innar tayi kwanciyar ta. TOP-NOTCH... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:04 Lekowa Inna Laminde tayi ta hangota d'are-d'are a gado, zaro idanu tayi cike da mamaki ta yafito ta da hannu. D'aga kafada tayi ita ba zata zo ba. "Kayya ni Laminde naga takaina. Tawo nan" ta kuma kiranta da hannu, juya baya tayi kamar ba da ita ake ba. "Sa'ade taso muje" tasan ba ji take ba da wannan kunnen, amma haka take sambatu da ta gaji da kanta, ta shiga cikin dakin ta dauko ta. Kuka ta saka tana niman kwanciya a kasa. Haushi da takaici ya cika Inna Laminde bata san lokacin da ta falla mata mari ba. Da sauri ta mike tana me kare fuskar jikinta yana rawa. Nuna mata hanya tayi babu shiri ta nufi hanyar tana kuka da ihu. Wanka ta mata har lokacin ihu take, "yau kuma sheganta kurma take ji?" Shiru Inna Laminde tayi bata kula shi ba. "Da Bara kika kaita sai kun samu tausayawar al'umma su bata sadaka." Banza tayi da shi ta cigaba da shirya yarta domin idan ta daka na Malam Aminu tabbas zata iya rasa turmin daka ta ta. Haka ta wuce dakin ta da Sa'ade ta shirya ta. Tsaf ta fito gwanin ban sha'awa hawaye ne ya zubo a Idanunta, mika mata kunu tayi ta sha. Amma tunda ta kawar da kai kamar taga kashi. Karshe fita tayi da jakar makarantar ta. Tana kuka har ta isa makarantar, tsayawa tayi a bayan ajin su zaune tana wasa da ƙara. Har aka fito tara tana wurin sai lokacin Halima da Nana yan ajin su suka zo wurin domin fitsari suka ganta zaune. Tana ganin su ta mike tana zare idanu, nufarta suka yi dama tana jin haushin an korota makaranta. Halima tana zuwa ta shure ta, bata kulata ba itama Nana ta maketa, tana mikewa ta kama kan Nana da hijab din ta shake ta, baki daya ta musu barin mahaukaciya, ta daki wannan ta daki wannan, sosai take jibgar su har sai da aka taru akan su, kafin aka wuce da su office din headmaster, duk suka durkusa. Ita dake bata da bakin magana shiru tayi, su da aka tambaye su, suka mata sharri, haka yasa aka zane ta domin sun fada bata zo makarantar ba, hakan ta fito daga office din tana kuka me mugun ciwo, kana jin kukan har cikin kanka. Aji ta wuce ta zauna tana shashekar kukan. Har aka tashi bata fasa kukan ba, koda ta dawo tun daga nesa ta hango Baffan dan dole ta share Idanunta tare da hàdiye kukanta, domin tasan ba karamin abu bane ya rufe ta da duka. Dake juma'a ce babu makaranta sai ranar monday. Suna zaune da abokan shi ana hira tazo ta wuce abin ta. Tana shiga cikin gidan ta samu an gama dafaduka, dakin su ta wuce ta cire kayanta, ta fito ta dibi ruwa ta wuce ban daki tayi wanka. Sannan ta koma daki ta saka kayan juma'ar da Innarta ta cire mata wata English me abc. Wanda Yayansu Ya'u ya musu sallah bara, sai farin hijab ɗinta yayi mata kyau, fitowa tayi dauke da abin sallah tana kallon Innar su. "masallaci zaki?" Dake ta juyo kunnen da take ji, gyada mata kai tayi. "Zauna kici abinci" motsa bakinta tayi tana girgiza kai. "Kin koshi ne?" Gyada kai tayi, dama tasan halin ta matukar tayi kuka bata iya cin abincin sai dai tayi ta fushi. Duk ranar juma'a yayan sun Iro yana turo me mashin ya kai su Binji suyi sallah da kwana biyu a can, kayanta kala biyu ta dauka suka fito domin yaron da iro ya turo ya iso. Ita kan burinta ba zata zauna a garin Binji ba, domin sokoto zata ta kai karan Innar su ta mare ta. Dama Inna Laminde tasha jinin jikinta tunda ta dake ta, yau zata tafi har Sokoto kai kara, tunda juma'a ce. Haka suka tafi Inna Laminde tana d'aga musu hannu. Dariya tayi tana faɗin, "Allah ya shirya min ke adawo lafiya daga kai kara da yaji." Lokacin da suka isa su Rabi da Harirah suka wuce gidan Yayarsu da sune ciki ɗaya. Ita kuma ta zuwa Ibrahim rigima, babu yadda ya iya dole ya bar shagon a hannun Yaran shi, suka tafi anan take son gaya mishi abin da Inna ta mata, sai misali take mishi bai gane ba. ^°°• Kallon Yarima Sadeeq yayi yana shirya mishi kayan sa, murmushi yayi ya tashi daga kwanciyar da yake yana daukar wayar hannu ya zuba idanu hoton wata kyakyawar budurwa ce akai tana da kyau me sanyi, gata kamar baturiya, danna kiran wayar yayi ya kanga a kunnen shi, har lokacin wayar a kashe take. Kiran Ummin shi yayi yana sallama. "Ubana kana lafiya?" "Ummina baki da lafiya ne?" "A'a kewarka nake" "Ummina" ya kirata a shagwab'e kamar zai tashi sama, murmushi tayi mishi sannan ta ce mishi. "Auta baka san ka girma ba ne?" "Ummina!" "Na'am Ubana" "har yau ni babynki ne" ya fada yana narkewa kamar yabi kasa ya kwanta , sake baki Sadeeq yayi yana kallon ikon Allah, abin shi mamaki ya ba shi. Dama haka Aliyu yake, "Ga Ummu Aymana" "Bata Ummina" wayyo Allah, anan Sadeeq ya gane me ake nufi da d'an Auta domin shi Auta ne amma babu irin wannan shakuwar da yayin shi mata da maza. "Didihhhh" ya kirata kamar ana tsikarar shi. "Na'am Autar Ummi" sake narkewa yayi yanar zai shiga wayar ya ce. "Didih, kin ji wai sun tura ni wani gari can me ma sunan garin Sadeeq?" "Maikulki" Sadeeq ya bashi amsa. "Kin ji wai Maikulki" "Allah sarki auyoo my Baby brother" yatsu ya dunkule ya saka a baki, "you pity for me?" "Mugun tausayi ma kuwa, kanina me nauyin chequer billion goma za a tura wani ƙauye" ta fada muryata yana rawa. Murmushi yayi, "ya isa haka ba sai kin yi kuka ba, ina kewar ku ne, don Allah ina Babyn baby?" "Hmm bata nan idan" "me yasa kuke boye min ita, me yasa idan na tambayi Ummina sai tace bata nan please meke faruwa ne? Na kira Dad yaki picking kirana." Ya fada kamar zai yi kuka. Amsar wayar Ummin su tayi tana faɗin. "ka kwantar da hankalin ka in sha Allah zata dawo" "but Ummina " "kana son nayi fushi ne?" Girgiza kai yayi kamar yana gabanta. "A'a " "Allah ya maka albarka " daga haka ta kashe wayar. Jikin shi ne yayi mugun sanyi, wannan shi ne karo na biyu da duk lokacin da ya bukaci magana da Ummu Mansurah ake hana shi magana da ita. "Sannu nace sannu Aliyu" murmushi "yawwa Yarima Sadeeq " sai kuma suka fashe da dariya. ^°°• International hospital Abuja Nigeria. Cardiac department. Zaune yake a gaban Babban likitan zuciya, yana wasa da wayar shi. "Mr Abdulhakim! Ka cigaba da shan maganin babu abin da ya samu aikin da aka yi a zuciyar sai ma nasarar da ake kara samu. Amma dole ka kiyayye damu sannan kana yawan motsa jiki domin bawa zuciyar damar aikin da ya da ce." Ya fada yana ajiye takardan da yake dubawa. Murmushi yayi yana shafa kasumbar shi. Sai da ya lumshe idanun shi , sannan ya bude idanun shi akan likitan ya ce. "Dr kana nufin an yi nasara kenan?" "In sha Allah anyi nasara yadda binciken ya nuna min " "Alhamdulillahi, duk da bana cire tsammanin daga rahamar Allah, amma nasan na kai matakin da dole na jira ikon Allah, na gode sosai." Rubuta mishi magani yayi , tare da mika mishi. Sake musabaha yayi sannan ya amshi takardan ya nufi inda motar shi ya ke, escort din shi ne suka taso suna bin bayan shi har inda motar su yake, suka bude mishi ya shiga yana sauke ajiyar zuciya. Duba wayar shi yayi wanda ya bari a cikin motar. "Seven miss call" ya furta a hankali, duba kiran yayi. Mother kurawa fuskar wayar yayi idanu, kafin ya dauke yana shin wani irin yanayi kafin ya kira layin."Abdul ina ka shiga ina kiran ka baka dauka ba?" "Kiyi hakuri na shiga meeting ne" ya furta a hankali, kamar ba zai magana ba. "Toh yayi maka kyau, kaga sakona a wurin sakataren ka?" Lumshe idanun shi yayi, yana jin wani irin nauyi a zuciyarsa. "Baka ji me nace ba ne?" Ta fada a fusace, domin tana da mugun zafi. "Ina jin ki Mami!" Ya furta a sanyayye. "Na ce kaga sakona a wurin Mubarak?" "Eh na gani, sai dai zan zo sokoton don Allah ki bani damar haka" yadda yayi maganar a hankali yasata saukowa domin tasan bai da wadataccen lafiya. Ita kanta ba don ranta take mishi haka ba, sai dai Abdul ya girman da yake bukatar iyali a tare da shi kodan lalluran shi. Dole ya ajiye mace a tare da shi."Allah ya baka lafiya, and likitan ka ya turo min sakamakon binciken lafiyar ka don haka ka dawo da wuri, domin a tsayar da magana ɗaya." " Toh Mami sai na zo" sai da ta kashe wayar ta, ya wurgi da na shi wayar. Baki daya an mai da shi kamar dan Babyn wasan Yara, bai da cikakken ikon kan shi sai yadda Mahaifiyar shi tayi da shi. Hatta matar da ake son ya aura muradun mahaifiyar sa ce ba muradun shi ba. Mahaifin shi ya xama kamar hoto sai yadda aka yi da shi, koda yake ai ba wani abu bane tunda haka ya taso ya gani. Duk da mahaifin su babban ma'aikancin gwamnati ne da ya rike manyan mukaman gwamnati har yayi retired aka kuma dawo da shi aiki. Cikekken sunan shi Abdul Hakim Sharif Hamidu, shi ne cikakken sunan shi a sanin shi dai tun farko auren iyayen su kamar babu soyayya da shakuwa. Sai dai biyayya ga iyaye domin yadda Mami take over acting yasa suka fahimci haka. Shi kuma irin wannan auren a gaban uban kowa mace tana iya nuna maka bata sonka. Domin a yadda ya samu labari mahaifin su yaron gida Alhaji Abdul Hakim bakasanmatsi ne me kamfanin gidan siminti na sokoto baki ɗaya. Tun kafin y aurawa Sharif Daulah ya nima mishi aikin gwamnati a babban mataki, yadda ba zata rena Sharif ba. Sai dai kash duk da wannan bai hana ta mugun rena shi ba. Domin Hajiya Daulah irin mata masu mugun izza ne da jin kai. Shi kuma irin mutane ne masu hakuri da sanyin hali. Wannan halin na shi da mahaifin Daulah ya gani ne yasa shi ba shi auren yar shi domin ko bayan ran shi zai yi wuya ya wulakantata. Sannan ya kuma fahimci Sharif bai da son zuciya domin yana da kokarin niman na kan shi, haka yasa shi nema mishi aikin gwamnati kafin Auren su. Duk da haka Sharif ba tsira a hannunta ba. Za a iya kiran auren su da suna rabo. Domin rabon Yara ne ya tara su zama inuwa ɗaya. Abdul Hakim shi ne babba suna kiran shi Abdul, sai Sadikkah take bin shi sai Afiyyah sai Taufiq, idan ka cire Abdul shi ne ya dauko halin mahaifin su. Sauran duk rashin Mutuncin Hajiya Daulah suka ɗauka. Lokacin da aka yi auren su ta tashi hankalin kowa har da shi mijin, ana ta samu cikin Abdul wanda tayi ta shan maganin zubda ciki. Amma Allah ya nuna mata ikon shi ta hanyar kare cikin har ta haife shi, sai dai kuma an haife shi da ciwon zuciya, sakamakon magungunan da tayi ta durawa da cikin shi. Har kasar waje Alhaji bakasanmatsi ya kai shi ya bude mishi file, duk bayan wata uku suna kai shi. Karshe da yaga zirga-zirgan yana yawa sai ya nima musu gida a can domin a lokacin babu me kudi irin shi, haka ya nimawa surukin shi damar ya karo ilimi itama kuma tayi karatun ta. Yaso tayi karanci bangaren jinya domin D'anta, amma fir taki sai kasuwanci ta karanta. A can ta haifi Sadikkah, rasuwar mahaifinta yasa suka dawo sokoto. Inda ta kafe zata tsaya akan kamfanin mahaifinta. Kasancewar ita ce yar shi daya tal..... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:05 Ganin ita ɗaya ne yasa take mugun jin kanta, ta kafawa kanta giggiwa da wani irin izza, bata san kome ba sai niman kudi. Domin bayan dawowarsu amsar kamfanonin ta tayi ta cigaba da kula da su, koda wasa Dr Sharif bai saka kan shi cikin duniyar ta ba, gudun kar a samu matsalar reni. Hajiya Dawlah ta rena talaka, ba a bakin kome yake a wurinta, shi yasa Yaranta suka taso da bakin kiyayyar talaka, idan ka cire Abdul babu ruwan shi, a duniyar Hajiya Dawlah kudi yafi kome daraja, shi ya sa bata harka da kananun mutane, sannan duk tsiyar mutum be tab'a zuwa inda take. Akwai gayen da ya nime auren Yarta Sadikkah, duk da suna son juna be hana da Hajiya Dawlah tasan bai da kumba susa ta mishi fata-fata ba. Idan kana Niman me kin jinin talaka toh wallahi tana sawun gaba. Duk da tarin dukiyar da Allah ya bar mata, akwai abu daya da tayi akan Abdul shi ne tura shi jami'an A.B.U zaria anan yayi degree din shi na farko, duk da a lokacin masu kudin da suke tura Yaran su, kasashen waje, ita bata tura shi ba koda mahaifin yayi magana cewa tayi. "Su makarantun can koyarwar suke da practice anan kuwa koyarwar su theory ne. Duk dalibin da ya samu tarkada daga makarantun nan guda, A.B.U, A.T.B.U, B.U.K, Udut. babu inda zai shiga ba a nime rike shi ba, domin jami'o'in sun san me suke kuma suna da good stander." Ba yadda ya iya da ita, haka ya hakura ya zuba mata idanu, domin yanzu yana fara magana zata ce kome sai shi yake da iko yayi. Kowanni Uba yana da burin ya tsaya akan Yaran shi amma Dawlah taki barin shi ya tsaya a kan yaran shi, sam bai san soyayyar mace ba, har sai da Allah ya haɗa shi da wata yar katsina me suna Fareedah, sun je wani aiki ya hadu da ita, kuma cikin ikon Allah sai aka yi dace itama daga babban gida ta fito. Auren shi da Fareedah shi ya janyo rigima wanda har Hajiya Dawlah ta bar mishi gidan ta koma gidan mahaifin shi, shi kuma ya zuba mata ido, don babu mahaifin ta ba zai iya wulakantata ba, shi yasa ya bar ta da halin ta, ana cewa kowacce mace da Arzikin ta a lokacin faduwar shi da Fareedah, ya samu manyan mukamai masu ban mamaki, domin sai da ya rike daraktan a majalisar dinkin duniya, uniter Nation. Allah sai ya nunawa Dawlah duk abin da take ji da shi yana ji dashi, dukiya ilimi, suna da daukaka. Amma a kullum cewa take da bazatarta yake rawa. Allah ya albarkaci Fareedah da yara uku, biyu maza mace daya. Fareedah tana da kirki hakuri da kawaici uwa Uba, biyayya da sanin kan namiji. Sai Allah ya haɗa jinin su da Abdul wanda shine yake rike da kamfanin simintin Mahaifiyar shi, ta tsani taji Abdul yana magana da Fareedah, tayi ta fada kenan Abdul baya kaunarta yafi kaunar mahaifin shi da matar shi. Daga ita har Yaran ta sauran babu ruwan su da Dr Sharif sai Abdul shima Abdul don babu yadda ta iya da shi ne. Domin yana gama degree din shi Mahaifin shi ya tura shi Canada ya tafi yayi masters din shi. Duk da bai da lafiya, amma yana da kokari. Wannan shi ne kaɗan daga Abdul Hakim Sharif Hamidu. •°°° Fadar Sarkin Kwara. 5:30pm. Mace ce dattijuwa, tana sanye da atamfar super neuver. Tasha ruwa da jin jiki saboda yadda tayi haske, wai ma don zanin babba ce yasa bata yagalgyale ba, yadda suke tafiya zaka rantse da Allah gidan zasu bari. "Iya kina ganin fadar gaskiya zai kubutar da ni? Iya ina matukar jin tsoro" juyawa tayi tana kallon shi, jikanta ne wanda iyayen shi suka rasu suka bar mata shi. Yazo da alamari me girma, taya zata yi shiru. "Kabiru taya zamu yi shiru bayan masu laifi suna raye baka gan su ba ne." Rintsa idanun shi yayi. "Iyah mu hakura don Allah, mu bar masarautar nan" "ko daya haka ba zai faru ba" ta cigaba da tafiyar ta, kamar zata kifa. Tana isa sashin Sultanah Badi'atul Noor, wacce ake mata lakabi da Sultanah karama. Suka jan tunga suka tsaya, "Gajiyah me ya kawo ki bangaren Sultanah karama?" Sarkin kofa ya tambaye ta, kasancewar an bashi umarnin tsaya a kofar sashin Sultanah tun faruwar al'amarin kisan Ummul Mansurah da ake zargin D'anta da yi, Sultan Abdulrahman Dan Aliyu Sulu Gambari ya hana kowa shiga wurinta, kuma kar a bari ta fita sai da dalili. "Sarkin kofa, alfarma nazo nima ina son ganin Sultanah" kallonta yayi Gajiyah mutuniyar kirki ce, ba zai iya hana ta shiga ba, don haka ya ce mata. "Kin san dokar hana shiga da fita da aka kafa, don Allah kar ki jima a cikin sashin domin Sultan zai iya zuwa kowani lokaci " gyada mishi kai tayi cikin farin ciki" In sha Allah ba zan wuce yadda kake tunani ba." Bude mata kofar sashin aka yi, ita da jikanta suka shiga cikin sashin. Zubewa bayi suke suna gaishe ta. Domin ita din jakadiya ce ta Sultanah Babba. "Gajiyah kece yau a bangaren Sultanah karama?" "Eh wallahi nice Zuwairah ina uwar dakin take?" "Tana lazumi ne" shiru suka yi kafin tace. "Don Allah ki nima min iso alamarin ujula ce" shiru tayi kafin ta ce mata. "Shi kenan bari na mata magana" wucewa tayi cikin babban falon, can ta wuce hanyar upstairs din, hango Iyatuh tayi dauke da kayan wanki. Murmushi tayi mata ta ce mata. "Sannu da kokari Yar nan?" "Yawwa Mama Zuwairah." Ta wuce dakin Sultanah Badi'atul Noor, ta bude a hankali, Aljannan duniya kenan. Duk inda ake niman kayan alatu na rayuwa ya samu a falon, katon hoto ne ita da Yaranta biyar. Maza uku mata biyu. Fuskartar ce juya ta jimami, wucewa tayi har bakin kofar ta buga. Gyaran murya aka yi, bude kofar tayi bakinta dauke da sallama. "Assalamu alaikum " ajiye Alqur'anin hannunta tayi tare da zare glass din idanunta ya zubawa Zuwairah ido" zubewa tayi a kasa tana mata kirara. "Barka da warhaka, uwar dakina baya giya marayu, me uban ma kin goye shi, Uwargidan Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, takawarki lafiya Giwa me tafiyar kasaita, Barkan ki da hutawa uwar zakuna uku, Babar Didih da Addah, Mamar Hamma Bubah, Uwar Sanda Babuga. Makiyan ki fadawar ki. Allah ya dawo miki da farincikin ki" zuba mata ido tayi, kafin ta ce mata. "Zuwairah da na jinki" gyara zama tayi sannan ta ce mata. "Ranki shi dade Gajiyah tana son ganin ki" "ki je idan aikota aka yi ta sako ne ta baki" "ranki shi dade, bana tunanin sako ne kamar ita da kanta tazo domin ta ce min ujula ce." "Tow ki mata iso" ta cigaba da karatunta, "na barki lafiya " ta juya ta fita, ajiyar zuciya ta sauke tana me jin kwalla na cika mata idanu. Duk Yaranta basu tare da ita, Zakiyyah da Rumaisah kawai take jin sauki daga gare su, Autan ma sun taso shi a gaba. Lumshe idanunta tayi tana tasbihi ga Ubangiji wanda ya cancanci girmamawa da bautawa. Tana zaune a wurin Gajiyah da jikanta suka shigo dakin, zama suka yi ta zuba musu idanu. "Barka da hutawa, akawala baki musaya, hankaka meda dan wani nata, alfadari kike me ado da zinari, maliya me ruwan alkhairi, Uwar Zakiyyah da Rumaisah, Hajiyar Abubakar da Umar, Innar Aliyu Abu turab, mun zo da babban al'amari ne me girgizarwa." Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta mai da dubarta ga kofar dakin ta. Juyawa Gajiyah tayi zuwa ga kofar dakin. Inuwar mutum ne a wurin. Mikewa tayi ta nunawa Gajiyah barandar da yake dakin ta waje, anyi wurin domin shan iska ne. Tashi suka yi tare da nufar wurin. Sai da ta rufe kofar dakin ta, bayan ta leka bata ga kowa ba. Sannan ta nufi wurin su ta rufe kofar wurin shan iskar. "Ina jinki " taryan-taryan ta labarta mata, abin da Jikanta Kabiru ya gaya mata. Mikewa tayi tana kallon waje, ba zaka iya tantance abin da yake ranta ba. Domin wani irin fuska take da shi, na ba zaka iya gane fushinta da farar ba, duk da ta kasance mace mara yawan fara'a. Amma tana da faran-faran da mutane, yanayin ta ne kawai ba me yawan fara ba, amma idan ta zauna a cikin Yaranta har da dariya take yi, tana da wuyar sha'ani ce. "Gaskiya ka fada Kabiru?" "Na rantse da Allah gaskiyar kenan" "shi kena, amma Gajiyah me yasa kika zab'e fadar gaskiya bayan kowa yasan ke kina tare da Sultanah Babba ce" hawaye ne ya zubowa dattijuwan, ta saka hannu ta goge tana fadin. "Koda ni ban rayu ba, ina fatan shi din ya samu kyakkyawar rayuwa, Sultanah ban zabi haka domin nima mishi alfarma ba, asalima ina son nayi amfani da haka ne niman kusanci da Ubangiji na, nayi wanka da zunubi, a yanzu kuwa ni da banza daya ne, don Allah ki taya ni kare rayuwar shi, wallahi bani da wani abu da zan iya kare shi" "zaki iya tafiya, shi kuma ya zauna a bangaren auta. Domin tunda kika kawo shi ba zan yi sake da shi ba. Shi ne shaidana" "Na gode sosai Sultanah " har zasu tashi ta ce mishi. "zauna kai" komawa yayi ya zauna yana kallon kasa. "Zaki iya tafiya " zama yayi, ta zuba mishi idanu. Kan shi a kasa, kafin ta ce mishi. "Kana son zama a nan?" "Eh...eh... Sultanah " ya fada muryan shi yana rawa. Murmushi tayi tana kallon shi. *Idan na sake ya bi kakar shi* "Sultanah abubuwa daya sun faru a cikin masarautar nan don Allah ki hako wasu domin kyautatawa ce haka" kallon Gajiyah tayi sannan ta ce mata. "Ba zan iya hako abin da zai mai da kasa ya binne ni ba, wanke Yarona kawai nake son yi ba tada abun da ya wuce ba." "Idan kuma kina da alaka da hakan fa?" Gajiyah ta wurga mata tambayar. "An san da wuyar biri bai hana a daure shi a kugu ba, akan me zan saka kai na cikin abin da ya wuce babbar matsalata wanda ya kashe Yarinyar da babu ruwanta, sannan aka jinjinawa Abu Turab" "Sultanah" "don Allah ki je" sultanah ta fada. Har ta isa bakin kofar sai ta tsaya tana kallon Jikanta da Sultanah. "Wata rana zaki so ki san me ya faru, idan wannan lokacin yayi, ki ziyarci garin ka'injin don Allah " "Allah ya nuna mana," "Ga amanar shi nan" "Allah ya taya ni riko" ta fada. Tafiya Gajiyah tayi, bai zama dole ta rayu ba, amma ya zama dole ta gayawa Sultanah gaskiya, tana fita daga cikin sashin ta kalli Sarkin kofa ta ce mishi. "A gafarce ni mai kofa." "Ba kome, amma kin san zuwan kinan akwai hatsari ko?" Goya hannunta tayi a baya, "me yafi ciwo a ce kayi bauta a maida kai saniyar ware? Ka tab'a gane cewa kalilan ne a masarautar nan suka san amfanin mu? Ko kasan." "Gajiyah abu shida ke aiki a Masarautar nan, Kudi, mulki, hassada da makirci, mugunta da kwadayi, don Allah ki cire hannunki a wannan al'amarin" "Bakwai ne Sarkin kofa, fansa kowani bangare burin shi fansa" "don Allah ina baki shawaran ki cire hannunki a cikin wannan lamari, domin kin manta da Cin amana, wnada ka yarda da shi zai iya cin Amanar ka akan kuɗi da zai kare, akan dan abin da bai da tabbas, don Allah ki janye hannunki" tafiya tayi bata ce kome ba. *Haka ne duk abin da muka lissafo shi ne yake faruwa, idan har akwai abin da zai faru tow ba makawa yakin gaba da Sultanah ce, ita ce abin harin kowa ita da Yaranta maza uku, an fadi a kan Abu turab, shi ma ai don yana tare da ita ne, ta iya kare shi tun daga yarintar shi.* Wannan shi ne zancen zucin da take tabbas yaran sultanah sune ake hari kasancewar sune manyan... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:06 Bayan fitar Kabiru daukar wayarta tayi ta shiga niman layin mahaifinta. Bugu biyu yayi ya dauka, "Baffa!" "Na'am Noor!" "Yanzu aka zo min da wani al'amarin da ya shafi mutuwar Mansurah" "Alhamdulillahi, ki saurare ni maza kar ki yi kasa a gwiwa waɗanda suka aikata haka sun san me suke yi ba jahilai ba ne, don haka kowacce kankantar hujja boye ta zasu yi." Mikewa tayi ta fita tare da budar kasa, bata yi wasa da wannan damar ba, kai tsaye ɗakinta ta nufa domin nan dakin hutawar ne, alkyabar ta dauka ta nufi heeram, bangaren Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari. Duk inda ta gifta zubewa bayi suke tare da mika mata gaisuwa, yadda zaka fahimci tana da mugun matsayi a cikin Masarautar. Bangaren Sultan yafi kusan kowani bangare girma da tsaro, domin bayan fadawa akwai sojoji da civil defense, akwai mopol, bata yarda ta bi kofar baya da yake cikin gidan ba, so take tayi amfani da damar ta, wanda ita kadai tabarwa kanta sanin shi, yadda ta sauya ba zaka tab'a cewa akwai abin da yake damunta ba. Yadda ta sake tana amsa gaisuwar, "A hanyar isa farfajiyar heeram suka yi kicibis da Hajiya Turai, ita ce matar Sultan ta uku. " Kallon juna suka yi kowacce da abun da ranta yake kitsima mata, musamman ita Hajiya Turai da take tare da bayi da kuyanginta suna take mata baya. Duk da kallon farincikin da takewa Sultanah Badi'atul Noor, sai dai har yau tana mamakin girman halinta. Zubewa bayin Hajiya Turai suka yi suna "Barka da warhaka Giwar mata, Barka da maraici magajiyar Sulu gambari." Cikin wani irin yanayi na nuna ita din ce suke gaisarwa ta juyar da kanta izuwa gare su ta ce. "Allah ya albarkaci rayuwar ku, Turai da fatan kina lafiya" "ke baki da damuwa ne? Kin san bana kaunarki amma kika matsa min dole sai kin shiga damuwa ta, ko kunya baki ji ba, kin dibo jiki zaki tafi wurin Sultan da yace baya kaunar ganinki a bangaren shi." Wani irin blush tayi tana kara daidaita nutsuwar ta. Matsawa tayi sosai suna fuskantar juna ta ce. "Ko shi Abdulrahman bai da ikon korata idan na shiga idan kin Musa muje ki gani" ta fasa ƙasa ƙasa yadda bayin da suke bayan Hajiya Turai ba zasu ji abin da yake fada ba. Sannan ta gyara alkyabar ta, tayi gaba abinta tana murmushin karfin hali. Gidan sarauta sai ka iya takun ka, sai ka iya adana fushin ka, sai ka iya makirci sai ka iya kissa da kisisina. Bude mata kofar suka yi Hajiya Turai ta bi bayanta da idanu, an dadde ana ruwa kasa yana shanyewa, tun kawo ta gidan kusan shekaru goma sha biyar har yau bata taɓa ganin macen da ta iya wanka da ado ban mamaki kamar Sultanah ba, kuma har kwanan gobe babu wacce take irin wankar ta, karya ne babu abin da zuciyarta ya gaya mata kenan, shi yasa ta tsane ta mugun tsaya, tsabar iyayi irin na Badi'atul Noor bata yawo da bayinta ko daya. Wai a haka ma don Sultanah Babba tana tsaye kenan amma baki daya Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari bai da nutsuwa matukar abin da ya shafi Sultanah karama ce, kwafa tayi ta nufi hanyar cikin gidan ta kofar baya, leshen jikinta ruwan makuba ne, amma matar nan dan tsiya ta haɗa mishi golden alkyabar wanda ya dace da ingancin shigar jikinta, ga wani fitinannen kanshi me sanyin dadi da yake tashi a jikinta, "Mtseeeeeew tsohuwar banza ta tsufa amma kullum zuciyarta na yara ne" kwafa ta kuma yi, bayinta suka kalli juna, suna kunshe dariyar su. Da sallama ta shiga babban falon shi, yana zaune a kasa, Sultanah Babba tana saman kujeran, Hajiya Bariyyah tana zaune a kasa, tayi kasa da kan ta. Gefe guda Hajiya Mariyah tana gefen shi, Amaryan shi. Sai Hajiya Suhailah, gabanta ne ya fadi Hajiya Suhailah Matar wan Sultan ne Sultan Abdulsamad Dan Aliyu sulu gambari, gefe guda Alhaji Marwan ne mahaifin Ummul Mansurah. Ji take kamar zuciyarta zata fashe,.asalima kamar ta juya amma kuma ma hakan zai iya janyo cece ku ce, wani malalacin murmushi Sultanah Babba tayi tana cewa. "Uwar dan gata,." "Hmmm, Sultanate masu abu da abin su kura da kallabin kitse, Allah ya kawo mu zamanin da ake yaki da gaskiya" "Aikuwa an zunguro inda ba za a iya ba." Wani munafikin murmushi Sultanah karama tayi, tana me jiman wuri ta zauna a saman kujeran, kamar yadda Sultanate ta zauna wato Sultanah Babba ita suke kira Sultanate. Kallon Badi'atul Noor Alhaji Marwan yayi. Yana mata alamu da ƙasa, domin shi kan Sultan ya kasa kome sai bin su yake da idanu, musamman yadda suke yab'a mata magana kuma murmushi take har tana washe baki, ba zaka tab'a cewa maganar su yana mata zafi ba, kallon Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari tayi cikin murmushi ta ce mishi." Allah ya huci zuciyar jan gwarzo ina bukatar ganawa da kai." A duk lokacin da ta ambace shi da jan gwarzo wallahi ji yake kamar ta dauke shi ta cilla shi wata nahiyar da babu kowa sai shi, kan shi sai yaji yayi rantalel, karkace kai tayi cikin iya kirsa ta fara wurga mishi kirari. "Wannan shine Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, Jan wuya Zakin talakawa Dodon azzalumai Lange Lange me kamar bazai je ba Nan gani nan bari dumamen mayya Kududdufin barkono iyakacin mace gwiwa Kaga Abba na Abubakar da Umar, Uban Rumaisah da Zakiyyah, Baban Aliyu Abu turab me takama da Hasbuballahu. Rankwatakwale ba shiga jirgin ba inda kan zai zauna Barka da Rana Mijina" jin shi yayi duk wani fushi da b'acin ran da suke tsakanin su ya kare, wato Ubangiji ya baka macen da zata kashe ka da takaici ta kuma rayaka da annashuwa arzikn ne. Kallon Mahaifiyar shi yayi da sauran jama'ar falon, ya mike yana faɗin "bari na gana da ita." Babu wanda ya ce mishi cikanka domin matukar Badi'atul Noor tana wuri wallahi babu wanda ya isa da shi. Yana gaba ta juya cikin murmushi ta ce musu. "Ba fada damu bane kwana mita." Daga haka ta wuce falon shi na musamman. Tana shiga ta same shi zaune yana wani haɗe rai, zubewa tayi a gaban shi, ta zuba hannunta akan gwiwar ta. "tun ranar da abin ya faru har yau baka ce min kome ba, ko da minti goma baka bani domin na gaya maka yadda muka yi da Baba karami ba " ta fada tana me isa gaban shi, "akan me zan baki damar magana? Bayan nasan duk abin da zaki fada wanke danki zaki yi? Idan maganar Babana ne ya kawo ki muje can na yanke hukunci." "Sultan ina son na gaya maka ɗazun na samu wasu bayanai ne na mutanen da suka yi kisan." Kallonta yayi sosai kafin ya ce mata. "Domin kare Kanki da danki shi ne zaki daurawa wasu sharri?" "Don Allah ka yarda da ni wallah......" Ƙarar tamburar masarautar suka ji sai da gabanta ya fadi, zubur ta mike jikinta yana rawa kamar zata tashi sama ta fita daga cikin falon yana biye da ita, sarkin gida ne ya shigo da mugun gudu ya zube a gabanta. "Sultanah an kashe Kabirun Gajiyah" luuuuu ta tafi zata zube cikin zafin nama Sultan ya riko kafad'ar ta, ta koma jikin shi, damuwa ta mata yawa tashin hankali yana niman kassara ta, janye daga jikin shi, ta nufi kofar da sassarfa ta nufi bangaren ta. Koda ta isa ga gawar Kabiru kwance cikin jini, window dakin Abu turab an balle shi, da alamu watsawa window ruwan battery aka yi, zubewa tayi a gaban gawar Yaron tayi, abin da kakar take gudu kenan. Juyawa tayi cikin matsanancin fushi da b'acin rai ta ce. "A tsare duk wani da me rai da yake numfashi a cikin gidan nan" "Babu wanda zaa tsare, da Abu turab ya kashe Mansurah cewa kika yi sharri ne bazai kashe ba, yanzu da kika saka a kashe dan mutane shi ne zaki fara borin kunya." A fusace ta juya tana kallon Sultanate da take maganar cikin fushi.Murmushi tayi sannan ta ce. "Ba laifi bane idan nayi hukunci a nan amma kuskure ne shiga cikin abin da yake mallakata. Sarkin dogarai! Maza a tsare kowa na ce" tunda aka fara al'amarin sai yau aka ga b'acin rai. "Wallahi babu wanda za a tsare" wani irin juyawa tayi tana kallon Sultanate, ja da baya tayi ita kanta a wannan gabbar kasa rike fushinta tayi, Sultanate zata yi magana Sultan ya ce mata. "Bangaren ta ne ko bata saka a tsare kowa ba, ni zan saka." "Au biye mata kayi abdurrahman kayi? Shi kenan Allah ya bada sa'a" ta futa daga cikin gidan, gawar Kabiru aka dauka aja fita da shi, ikon Allah ne kawai yake tafiyar da ita, amma tabbas yadda numfashin ta yake sama da kasa, zata iya faduwa domin baki daya karfin ta da kuzarinta ya kare, shigowa ɗakinta tayi, ta rufe dakin tare da shiga ban daki ta kunna ruwa, yana zuba a kanta. Bata son karaya amma tabbas abin da Baffa ya fada kenan? Da Gajiyah take cewa ta hako abin da ya wuce tow kuwa mutuwa zata yi. Bin bayan mahaifiyar shi yayi, tunda ta shiga falonta ta zauna tana huci. "Har ni abdurrahman zan nunawa ban isa ba? Yaushe aka haifi Badi'atul Noor da zata saka doka ya goya mata baya? Ni da na haife shi bai saurare ni b sai ita, wato bani da daraja." Shigowa yayi ya zube akan gwiwar shi, tare da dan durkusawa. "Badi'atul Noor ta fini daraja kenan? Ta fini kenan tow ka je kai da ita na bar mata kai, Hakkin Mansurah kuma zan kai ku kotu a nima mata hakkinta" fada take yi inda take shiga ba nan take fita ba, fada take kamar zata rufe shi da duka, tana gamawa ta wuce ɗakinta har lokacin yana durkushe. Bai tashi ba. Duk ya rasa inda zai saka rayuwar shi.. ** Sokoto. Yau lahadi, iro da kan shi ya zo har garin sokoto ya dauke ta, suna tafiya tana mita kome ta gani sai ya saya mata har suka Binji,shagon tela ya kaita ya amsa mata dinkin sabon uniform ɗinta. Kallon shi tayi ta daura kanta a kafad'ar shi tana jin ina ma da zata iya mishi bayani a ya maida ita Sokoto domin tunda ta je zero tension, babu tsana babu tsangwama. Har suka iso gida da magariba, da murnanta ta shiga cikin gidan tana jin kamar ta shekara bata ga innarta. "Assalamu alaikum, sannun ku da gida." "Yawwa iro ya can wurin ku?" Inna Larai ta amsa masa. "Alhamdulillahi ya muka same ku?" "Masha Allah, Bimbi an dawo kenan." Dake kunne me jin ta juya gyada mata kai tayi, ta shiga ware ledar ta mikawa Rabi da Harirah kayan su, sannan ta wuce dakin su. Inna Laminde tana sallah, ta koma gefe ta zauna. Ganin zaman ba zai kare ta ba, ta nufi waje tayi alola domin shima Iro masallaci ya tafi. Koda suka dawo tana kwance a saman cinyar Inna Laminde, bakinta dauke yake da magana da labarai amma ta rasa yadda zata bata su. Sai murmushi take, ita kuwa Innar ta dage sai mata hira take, dan ajiyar da tayi dauko wannan ajiye wancan har ya cika mata gaba da abinci. "Inna yanzu ita haka zata rayu babu me gane abin da take so?" "Allah almusawiru yana sane da ita, babu abin da zan iya sai abin da hali ya bamu" "Gaskiya akwai matsala wallahi ita zata iya ji da kunne daya amma ba zata iya mayarwa ba." "Ibrahim don ka rena ni, har ka dawo da wancan abar ba zaka gaya min ba" inji malam yana shigowa dakin, duk da taji shi, kara rufe idanu tayi tana rike zanin Innar ta. Shure kafar ta yayi ta mike zubur jikinta yana kerma...... [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Fatan Alkhairi Autar Manya ❣️😻😍 Page:07 "Don Allah Malam meye haka kake kamar yaro karami? Taya zaka shure ta kamar ka samu jaki?" Inna Laminde ta fada a fusace. "Yo ai tafi kama da hakan ne" kura mishi idanun suka yi, babu wanda ya iya magana domin iskancin Malam kara girmama yake, har ya gama shirmen shi ya futa bata ce mishi kala ba, "Inna kiyi hakuri wata rana sai labari in sha Allah Bimbi zata zama wani abu." "Hmmm Amin Ya Allah, tsoro na daya ne kar na mutu Bimbi ta shiga wani hali." "Ayya Inna babu wanda yasan gawar fari" "hmm" ta ce, suka cigaba da hiran su. Dake akwai dakin su na samari nan ya wuce ya kwanta. Washi gari da asuba, bayan sun yi sallah asuba. Daukar allonta tayi ta nufi hanyar waje da hijabinta. A tsakar da ta hadu da Innar su, dake aiki ya sha manta jan rigar ta tai, tana kallon ta. "Zaki makaranta ne?" Lumshe idanunta tai, sannan ta mata murmushi. Shafa kanta Inna Laminde tayi tana faɗin. "A dawo lafiya " murmushi tayi da ya fito da jerarrun haƙoranta. Ta nufi hanyar waje. A bakin kofar fita taga baffansu. Hàdiye yawu ko ta ya zata yi karatu ita da ba magana take ba. Asara yawun barci. Dauke kai yayi ya cigaba da jin labaran karfe shida da rabi na BBC Hausa. Yana wurin har Bakwai saura, suka dawo ita da yan uwanta. Kallon Rabi da Harirah yayi cikin farin ciki, "Allah ya muku albarka rabi da harirah." "Amin Baffa" wuce su tayi abinta, tana shiga wanka suka wuce, sai fushi take ita ba kome ya sata fushi ba iya iyaka yau Monday, kuma zata makarantar boko, sai ta fara jin ba dad'i. A can birnin Shehu kuwa, tun ranar Friday Prince Aliyu ya ga inda aka yi Poster din shi, amma yaki tafiya domin so yake lallai ya wuce Illorin, sai da Ummin shi ta mishi fada ya hakura, tun safe aka shirya dogaran da zasu raka shi, wurin karfe goma suka nufi bangaren Mai Martaba Shehu Abubakar Shehu, ya mishi nasiha da fada, sannan ya mika mishi wani takarda wanda shi kan sa Prince yake da yakinin kudi ne, godiya yayi sannan ya nufin inda ake jiran shi, koda ya isa bude mishi motar aka yi ya shiga, daga nan suka nufi Binji local government, gidan Hakimin Binji suka fara sauka anan aka kai su local government SC suka yi abin da zasu, sannan suka wuce Maikulki, a gidan Mai gari aka sauke shi a ɓangaren wani dan mI gari da yake aiki a lagos, dake ɓangaren ya fi ko ina a gidan kyau da tsari, ko dar Mai gari bai ji ba, yasa aka gyara mishi daya daga cikin dakunan, flat ne mai mugun kyau da haduwa. Duk da an saka mishi kome a gidan sai dai babu wutar lantarki, tunanin shi ya tsaya ne lokacin da ya zaro laptop din shi, da wayar shi. Fitowa yayi yana murmushi domin yara sun cika bangaren wai sun ga baturen cikin tv. A hankali ya fito. "Yallabai me kake bukata?" "A'a Baba Abu turab zaka kira ni, nima d'anka ne." "Wane mutum Yallabai dai, kana bukatar wani abu ne?" "Eh tow Baba" ya fada yana sosa kai, "me kenan?" "Hmm dama tambaya zan yi ana samun wuta ne?" "Eh amma ba sosai ba, kuma sai da nayi tunanin zaka bukaci wuta ko dan irin kayan aikin ku na zamani." "Eh Baba" "gashi babu." "Ba damuwa, bari na fita zamu koma Binji mu nemi injin" "tow madalla, dake kaga Habibu zuwa yake da na shi ya kuma koma da ita, da ya barta ai da na saka mai sai ka kunna don Allah kayi hakuri da yanayin garin mu" "ba kome fa" ya fada yana murmushi. Yara suna bin shi. "Kai ku b'ace anan" Mai gari ya faɗa. "Kyale su Baba." Ya fada yana murmushi. Durkusawa yayi yana kallon Yaran. Sai su kalle shi sai su koma da baya, "eh Bature na" sai su tab'a hannun shi su koma da baya, dariya suka ba shi ya mike yana faɗin. "Abokaina bari na je na dawo " "laaa kunji Yaren yake " ita kanta Hausar shi cewa suke yare na, yana fita fadawan da suka rako shi har biyu suna nan. "Kun san me? Zaku bar min motar ne kamar yadda mai martaba ya ce, zamu Binji sai ku wuce sokoto" ya fada yana wucewa gaban motar ya zauna a daya wuri me zaman banza, yana nazarin abubuwan da yake bukata. Lokacin da suka isa har tasha ya kai su, sannan suka fita ya musu alkhairi domin ya koyi haka daga iyayen shi, sai sa yaga tashin su, sannan ya koma kasuwa yayi sayayya, kafin ya juyo garin yaran nan kuwa kwalin biscuit da chocolate ya saya musu. Sai yar karamar gas wacce zai yi amfani da shi incase. Lokacin da ya iso ya shake motar da kayayyakin amfani da generator. A gajiye ya dawo lokacin ana sallah azhar, shi da wani dan me gari Nazifi suka sauke kayan shi bai samu jam'i ba. Haka suka nufi cikin gidan da kayan. Yana ajiye kayan yayi alola sannan ya nufi masallaci, sai da yayi Sallah suka kuma gaisawa da mutane, sannan ya shigo cikin gidan. Aka kawo mishi abinci bai saba ci shi daya ba, ko a Sokoto da mutane yake ci, domin ko a gida a tare da Ummin su da Ummul aiyman suke ci. Fitowa yayi yaga Yaran nan, daukar butar da aka kai mishi yayi ya kira su, suka wanke hannun su, sannan ya shiga dakin ya kawo musu praying mat. suka zagaye shi a tare suka ci abincin, kusan sune suka ci har da wawar su, murmushi yayi yana kallon su. Mikewa yayi suka biyo shi dakin shi, bude kwalin biscuit da chocolate yayi ya dauki wani laida ya zuba musu. "Kuje a raba muku kun ji" a guje suka fita suna ihu. Suna fita Mai gari yana shigowa, shima fita yayi zai tattara kayan abinciin. "Ba dai basu abinci kayi ba Yallabai?" "A'a Baba " ya fada yana murmushi. "Ga zahiri nan kamar an zubawa kaji abincin, nace ko zan kira maka wani Yaro ya taya ka haɗa wutar ne?" "Eh Baba " haka ya fita ya sa aka kira mishi lawi, suka hada wutar. Sai da ya kunna inji din domin da mai ya sayo abin shi, sai yaga iya bangaren shi ne da wuta. "Dan uwa,ko zaka iya hadawa da wutan gidan baki ɗaya " " ba matsala Yallabai " domin yana zuwa mai gari ua gaya mishi tow yarima ne daga Masarautar Sakkwato. A take ya shiga girmama shi. Komawa yayi daki ya kwanta, ya bar lawi da aiki. Sai da ya gama daidai ana kiran la'asar, suka fito tare. Mika mishi kudin aikin yayi ya ce."a'a yallabai mai gari ya bani" "karba nace" ya fada yana sassauta faraa shi. "Allah yasaka da Alkhairi" share shi yayi. Alola suka yi aika suka shiga Masallacin. Bayan sIlun isar da sallah, ya jima a masallacin kafin ya fito yana kallon garin yadda ya burge shi. Nufo shi mai gari yayi yana faɗin."ko zaka zaga garin nan na kira maka Nazifi" "Eh ba zan ki ba" kiran Nazifi yayi suka shiga zaga garin, har sai garin ya fara duhu suka dawo, a can hanyar rugar su Sa'ade suka samu wata saniya ta kasa, an yanka ana niman masu saya, abin ka da jini yana yawo a jikin shi, a take yasa domin yana da kauna tare da amana da tsakanin su da nama, shi yasa yana gani ya saya, abin ya faru akan idanun Malam,domin da aka yanke kudin saniyar bai zata A.A zai saya ba, sai yaji ya ce tow a biyo shi da saniyar zai biya. Sai da aka yi sallah magriba ya biya kudin, sannan mai gari ya saka aka nimo Yaran shi suka shiga gyaran saniyar. "Yallabai ya zamu yi da saniyar?" Mai gari ya tambaye shi, " a kai cikin gidan sai su fada abin da za a basu, ina son a soya min shi yadda zai kwana biyu sauran kuma a rabawa kowa da kowa." "Sannu bako me cida dan gida" tuwon shinkafa miyar kuka da yaji kayan kamshi, ga shi zabuwa aka burge a miyar. Sai tashin kamshi. Lokacin da yaga tuwon sai da ya kira Ummin shi, bata dauka ba. Kiran Rumaisah yayi. "Addah wai me yasa Ummina bata daukar kirana?" "Abu Turab Sultanah tana wani uzuri ne a wannan gabbar ka mata uzuri don Allah " "tow princess fa?" "Ka tambayi Ummina" ta gaya mishi tana kashe wayar ta. Domin karfin hali tayi ta mishi magana domin Ummin su, ta gargade su da kar wani ya gaya mishi. Halin da ake ciki, fita ya yi bayan aka ayi sallah isha ya dawo gida. Kunna inji yayi ya kwanta abin shi. iskar fanka yayi awon gaba da shi domin ya gaji sosai. Bai san lokacin da injin din ta mutu ba, domin tunda na Nazifi ya shigo ya samu yana barci wurin karfe biyu na dare sai ya kashe injin ɗin. Suma a lokacin suka gama gyaran saniyar, sai a sallah asuba suka hadu. "Kuyi hakuri na bar ku da aiki, sannun ku da kokari." "Ba kome wallahi, Ni na kashe maka injin jiya da karfe biyu na dare." "Hmm ka kyauta domin ma gaji ne jiya nima " sosai suka sake da juna kamar sun shekara da sanin juna. "Nazif gashi ka basu su sayi abin bukata da shi. " "Ai baba ya bada kudin su mangyada da sauran su " "wato ba zai huta ba ko? Tow don Allah ka basu, su kara in case" dake Abu turab yana da mugun cika idanu da kwarjini bai musanta mishi ba ya amsa. Shi kuma ya wuce bangaren shi da yaga an kawo mishi babban flask da karami. Shiga ban daki yayi ya dauki bokiti ya wanke tass, sannan ya juya ruwan, ya shiga dakin ya sauya kaya ya fito ya wuce ban dakin. Yayi wanka sannan ya fito ya shirya, anan ya kira Ummin shi, babu wani kulawar da ya saba samu sai baki daya yayi laushi. "Ummina nayi laifi ne kuke hukunta ni da abin da ban sani ba?" Ya fada idanun shi yana cika da kwalla. "Baba karami, kayi hakuri kayi abin da ya kawo ka. Wata tara kake da shi please ka tabbatar kayi abin da ya dace karka manta da alkhairi da sadaka" "in sha Allah" ya fada yana gyada kai domin yayi kewar ta sosai. "Ummina Ummul Mansurah" "kayi hakuri gaskiya bata nan na tura England wurin su yayan ka." "Shi ne ba ku gaya min da wuri ba." "Tow uban masu gida na gaya maka yanzu ko?" "Shi kenan zan tafi makarantar da aka turo ni." "Allah ya maka albarka, ya tsare ka da sharrin maraici da dare, ya hada ka abokan alkhairi na gari, kar ka manta da yin alkhairi tare da sadaka domin maganin masifa ce, yawan ta Alkhairi yana cika mizani, sadaka maganin masifa ce, yawan nafilla yana kara kusancinsa da Allah, don Allah kar ka cutar da wani domin ba iya kai zai tsaya ba. " Nasiha masu ratsa zuciya da jiki haka ta gama mishi fada, sannan suka yi sallama, shima ya fito. Cikin gidan ta shiga ya nufi bangaren da aka nuna mishi na uwar mai gari, ya gaida ita tare sa bata hakurin yazo ba shi shigo gaida su ba, sai aiki ya kawo. Cikin fara'a ta amsa mishi, "ba kome ai mun ga aiki kake yi shi yasa baka shigo ba, da fatan wurin bai takura maka ba." "A'a ba kome " "sannu da kokari mun ga tsaraban yara" "babu kome Umma" sauran dakunan yabi suka gaisa sannan ya mikawa Uwargidan mai gari key dinki shi. Kana ya musu sallama. Ya nufi waje ya samu an goge mishi motar shi, kafin ya kalli Mai gari. Ya ce mishi."Baba ai da kafa zan tafi naga makarantar babu nisa." "Tow shi kenan Allah ya dawo da kai lafiya." "Amin Ya Allah" ya nufi makaranta. "Yau naji labarin malamai daga Binji sun iso Allah ya baku damar ɗaukar nauyin yaran, akwai yarinyar da nake so don Allah ka saka idanu akan ta Yallabai" "ina jinka" ya tattara nutsuwar shi ya daura akan shi. "Yarinyar kurma ce bata magana kuma, akanta aka kawo ku," "babu wata gamayyar kungiyar Handicapped ne a nan?" Girgiza kai yayi yana faɗin"ko wancan satin na samu labarin uban zai fita da ita niman taimakon kan sa, kwana ɗaya nayi da kai na fahimci kome akan ka, ka taimaka mata shekaran ta goma baki ɗaya" shiru yayi yana kallon Mai gari kafin ya ce. "Allah ya bamu ikon taimaka mata domin kai ne sanadin haka" kallon Aliyu yake domin bai tab'a ji ko ganin matashi irin shi me saukin kai ba. Dan manyan mutane wanda kana ganin shi kasan kudi da mulki ya zauna a jikinsh. Sallama yayi Nishi. ------------ "Malam Aminu kana nufin Bature ne aka kawo garin nan?" "Ina gaya maka jiya a kan idanu na ya sayi saniyar da ta kasa a mutunce , da alamu me arziki ne." Inji Malam Aminu, gyara zama malam Musa yayi ya ce. " Kai haba? Kasan dai gobe zaka kai Yarka wurin niman taimakon nan ko?" ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:8 "Gaskiya kan gara na kara shi akan haka, daga Makarantar zan dauke ta" murmushi Malam Musa ya mishi tare da cewa, "kar ka manta idan aka samu me yawa kar a manta da mu domin mu ma, mu dangwali arzikn yar mu" dariya ya saka yana faɗin "haba ai kaf duniya bani da masoyi irin ka, duk abin da na samu na ka ne." Ya fada suna tafawa. Da ace Malam Aminu yasa yadda Malam Musa ya tsani ganin shi da ba zai tab'a ɗaukar shawaran shi ba, amma baki daya bai da aiki sai daukar shawarar shi, bayan idan suka yi magana shi yake gayawa sauran abokan su, su kuma su gayawa Mai gari, haka yasa Mai gari ya saka a aka kira mishi Malam Musa ya ci mutuncin shi, domin ya zama mugun aboki me son ganin bayan abokin shi da munanan shawara. .... Tunda ya bar gidan ya nufi makarantar, yara ke bin shi musamman yan mata masu tashen balaga. Abin ya basu mamaki yadda suka gan shi Bature dan gayu, kuma yana tafiya kamar mace a yangance, asalima shi mutum ne da bai da kazar kazar, haka yana nasaba da inda ya fito ne, duk da a dabi'ar shi babu maida hankali akan mulki, amma mulki da kasaita tana bibiye da rayuwar shi, hakan yana faruwa ne idan yana cikin damuwa, ko bacin rai tow hatta maganar shi na iya sauyawa. Aliyu Abu turab, dayawan mutanen da suka san tashin sa, suna mishi lakabi markabu iyalan gwamna, gadanga kusar yaƙi, bauna saniyar sake. Shigar shi makarantar ya hadu da malamai da suka zo daga Binji, wanda kana ganin su, kasan suma aiki suka zo yi, sallama ya musu ya wuce Office din Headmaster. Office din a rufe yake shi kan sa bai zo ba. Jingina yayi da bangon office din yana me sunkuyar da kan shi. "Burr-burrrrrrr" kara wata ya gulalliyar mashin kiran Yamaha ya shigo cikin makarantar, sau daya ya d'aga kai ya kalli headmaster sannan ya cigaba da tsayuwar shi, kafin headmaster ya shigo hayaniyar yara ya cika wurin. "Bata magana bata magana ohooo" dauke kai tayi kamar bata ga suna tsokanarta ba, sai a lokacin ya d'ago ya zuba mata ido, ita kanta yadda take tafiya zaka fahimci a takure take, sannan koda bai ga fuskar ta ba, ranta a b'ace yake. "Ita ce kenan?" Ya tambayi kan sa, wucewa aji tayi tana ta gaban shi. Kallon uniform ɗinta yayi yaga yadda yake daukar idanu, ba mamaki Mahaifiyar tana kula da ita. Nana ce ta bita da gudu ta kai mata duka, faduwa tayi ta mike tana kallon Nana ta ma rasa me zata ce mata, kawai ta juya tayi tafiyar ta. Shekaru goma baya haka ya ya faru da Ummu Mansurah. Murmushi yayi yana kallon su. *** Kalambaina estate Anan gidan Dr Sharif yake, tare da Amaryan shi Aunty Fareedah wacce suke kira da Aunty Mom. Tun ranar juma'a ya shigo Sokoto, amma yaki zuwa gidan Mahaifiyarsa. "Yaya Abdul!" "Na'am my angel me kike so?" "Home work aka bamu ban fada da wuri ba kuma yau zamu yi submit din shi" shafa kan ta yayi yana faɗin. "Na'imatullah me yasa baki gaya min tun jiya ba, na gani." Murmushi tayi, ta zuge jakar Yayanta me suna Hamidu yana zuwa ya make kanta. "Bata da hali aikin ta kenan ba zata fada tana da home work ba sai za a tafi school." Murmushi Abdul yayi ya ce mishi. "Kowa da kalar rayuwar sa" gyada mishi kai yayi, ko babu kome Aunty Fareedah da Yaranta suna saka shi farin ciki, madadin gidan su da ba barikin soja bane amma bin doka da oda sai a slow, gashi babu dan raha da farin ciki irin na gidan Aunty Fareedah. "Sannun ku babban Yaya da kanen shi" yar fara a yayi yana faɗin. "Aunty Mom kin ga yau Hamid bai rungume Ni ba" "oya wuce kayi rungume shi" "ayi hakuri na manta ne" yazo ya rungume shi ta baya. Abin da ya rasa kenan a cikin gidan su, yana buƙatar kulawa kodan irin laluran shi, fitowar commissioner of education, yasa suka juya yana saka links din hannun rigar shi. "Mr Hakim ka manta yau zaka koma bakin aiki? Ko so kake Hajiyar ku ta cinye ni danye?" Kallon mahaifin su yayi ya ce. "a'a idan na karya zan wuce." "Yaya kai zaka kai mu school?" "Kuna so ne na kai ku?" "Eh muna so, zan nunawa Jalilah nima Yayana yana sona" make keyarta Hamid yayi yana fadin "ke dai" kafin ya karasa ta ce mishi " baki da hali, sam baki da wani abu sabo, ko basu bane?" Ta mike da kofin tea ɗinta, ta nufi kitchen. Iyayen suka zauna. "bani Jakarta" mika mishi jakar Hamid yayi, ya saka mata. "Mamarka tace kaki maganar aure duk yarinyar da ta nima maka sai kace baka so" a hankali ya fara shan tea da Auntu Mom ta hada mishi. Yana sauraron mahaifin su, haka ma Hamid da ya nutsu yana sauraron mahaifin su. Wannan yana daga cikin abin da ya kara sakawa Alhaji Sharif Hamidu, kaunar matar shi Hajiya Fareedah, domin tarbiyyar Yaranta daban yaƙe, da ace a gidan Hajiya Dawlah ce, da yanzu yaran sun fara mishi shakiyanci da rashin hankali, ita kuwa Fareedah ko fada yake ba zaka tab"a jin tayi magana ba, asalima sai tayi shiru daga baya sun had'e a oda room, ka ga yadda yake susucewa yana bada hakuri. Tasan kan mijinta, wannan yanayin har Yaran ko fada yake musu, zasu yi shiru daga baya zaka ga sun bishi daki har suna kuka yayi hakuri, karshe kuma shi zai koma rarrashin su. Shi yasa gidan yake zaune cikin farin ciki. Haka Abdul shima dabi'ar gidan Aunty Fareedah ya kama shi, koda Hajiya Dawlah ke fada ba zai taba magana ba, tana gamawa zai ce mata kiyi hakuri. "Yana da kyau kayi aure, ka samu me kula da kai." "In Sha Allah zan yi yadda kace ayi hakuri" daga haka suka ci gaba da karyawan su, yana gamawa ya mike. "Hamid kace Widad ta fito mu tafi" "ok Sir" ya fita, "Abba ka daina mishi fada a gaban mu, mu kanen shi ne. Ba dadi" kallon Aunty Fareedah Dr Sharif yayi ya ce mata. "I did something else?" "Gaskiya ya gaya maka, kuna bukatar kebe wa ai" "Allah ya huci zuciyar Ubana ba zan kuma yiwa ɗan dan uwanka fada ba a gaban ku, don Allah kaso shi yadda yake son ku. Ya shirya ya bata da kowa saboda ku." "In sha Allah Abba, ke kucilili muje " ya kwalawa Widad kira, ta fito dauke da water bottle, ta nufi hanyar waje. Domin ya dauki jakarta, gaba ya shiga shi ya shiga baya. Suka nufi makarantar. Kiran Mother ya gani gaban shi ya fadi, ya taka birki da sauri. kallon shi suka yi. "Yaya lafiya?" "Lafiya lau yan uwana. " Haka ya cigaba da tafiya be dauki kiran ba, har suka isa makarantar, daga nan ya juyar da kan motar zuwa g.r.a gidan mahaifiyar shi. Tun a bakin kofar bayan ya ajiye motar yake jin tashin muryan ta.duk sai ya diririce. "Na zata zama zaka yi har abada a can, Nace na zata shiga cikin Fareedah zaka yi ta kuma haifarka, ni baka damu da ni ba, sai ita yadda ta tsafe Ubanka shi ne zata tsafe min kai na rantse da Allah baku isa ba, nace baku isa ba" yadda take bala'i kamar zata doke shi bai saka ya ce mata cikanka ki ba. Haka ta gama yana kallon Kannen shi, kowannen su harkan gaban shi yake, a gefen shi Taufiq ya dauki wayar shi da kayan makarantar shi ya fita sannu wannan bai ce mishi ba, tana mita Afiyyah ta fito itama ko kashi yafi shi daraja, haka ta fita sai cewa tayiwa Uwar "Hajiya na tafi" "tow" kallon ta yayi bayan sun fita ya ce mata"kiyi hakuri" bayan ya hàdiye wani yawu me daci, taya za a ce kanen ka babu shakuwa da soyayya a tsakanin ku. "Ka karya ka wuce aiki" "tow" har ya mike ta kalle shi."kana shan magani kuwa?" "Eh ina sha" "tow ya batun aure?" A duburce ya juya yana kallon ta. "Nace ya batun aure?" "Hajiya dama-dama- dama" "Abdulhakim na baka kamfani na ka rike bawai don ban san ciwon shi ba ne, iyalin zaka ajiye kamar kowa sai a wuce wurin" zama yayi yana saka hannun shi a tsakanin cinyar shi ya ce mata." Hajiya yan matan yanzu suna da buri, Hajiya rayuwata babu buri dayawa, babban burina na samu macen da zata so ni, bayan nan mu gina rayuwar mu cikin farin ciki da jin dadin, bana son tashin hankali idan kika matsa na auri yan matan zan aura amma babban matsalar farin cikin da nake son samu bai zama dole ba, ki kara min lokaci, kafin ayi min aikin karshe ina sha Allah zan gabatar da matar da nake so " shiru tayi tana kallon shi, so take tayi magana amma kuma wani bangare na zuciyar ta yana gargadin ta, da tausassa mishi. "Alright zan duba al'amarin aikin da zaa maka zai dauki 4 to 5yrs Inci gaba da ganinka babu d'a babu mata? Akwai adalci a nan?" Kamar ya fashe da kuka ya ce. "Hajiya likita bai miki bayanin yanayin ba ne?" "Idan ya min bayani sai na dauka? Ko ce maka aka yi can believe da abin da suka ce? Look ina son naganka cikin iyali da wadata wanda haka ba zai samu ba, sai kayi aure " "tow hajiya " zanyi yadda kika ce. *** Kwara Dukkan familyn sun hadu, a cikin su har da Sultanah karama da Sultanate, babu abin da suke bukata kamar Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari ya zartas da hukuncin shi akan Aliyu. "Binciken da aka yi, ni na yanke hukuncin a duk inda aka ga Aliyu a kashe shi, shi ne adalcin da zan iya samarwa " ya fada a matukar sanyayye. "Gara a kai shi kotu domin zan daukaka kara." Ta fada cikin kwarin gwiwa. "Badi'atul Noor!" Baffanta ya daka mata tsawa. "Kayi hakuri Baffa batu ne na D'a nasan idan da Marigayi ko mahaifina suna raye za a samar mana da adalci tare da zakulo gaskiya. A daren ranar tana bangaren Sultanate sannan ta turowa Baba karami sako, yazo ya dauke ta. Sannan bayan nan mutuwar ta, ta turo min sako Ummina ki taimakawa Abu turab kar ya ci kome da za a kawo mishi an shirya ciyar da shi guba, ga sakon nana cikin wayata. Sannan kafin mutuwar ta, inda aka kashe ta daban inda aka ajiye gawarta daban, hujja ta karshe kashe Kabirun Gajiyah da shi idanun shi ya gane mishi kisan da aka yi, sannan itama Gajiyah aka illata lafiyarta yadda ba ta san waye akanta ba." "Badi'atul Noor hujjar kare danki ne duk wannan surutun?" Kallon Hajiya Suhailah yayi kafin ta ce mata. "Bani da buri ko yau Abdulrahman ya fadi Yarana sai naso su zauna a cikin gidan nan, balle kuma kun ga wani a cikin su bayan Baba karami? Ku sani ina shiru ne kawai don bana son magana, Uwa madubin goben D'anta Na amince da duk hukuncin da zaka yi, a cikin hukuncin har da sauke ni a matsayina, tare da sauwake min matukar zaka janye kalaman ka akan shi na bar kome na cikin gidan nan na yafe kome, amma daga ranar da gaskiya tayi halin ta, tabbas a lokacin zan zartas da nawa hukuncin.... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:9 "Meye nufinki Badi'atul Noor? Don na kyale ki ba wai yana nufin kin fiyi abin..." Kura mishi idanu tayi, tana murmushin karfin hali. Bata son ta nuna gazawarta a matsayinta Na uwa bata son ta nuna kasawarta a matsayin ta na Mace me daraja a wurin kishiyoyinta, don haka ta mike tare da tattara alkyabar ka, "Sultanate kece kika haifi Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari." Takawa tayi har gaban ta tana faɗin. "Ki gaya mishi na bar miki ɗan ki, domin nawa rayuwar d'an, idan wani abu ya faru da Aliyu Abu turab. Masarautar nan tayi mana kadan na rantse da Allah" daga haka ta juya ta fita bata kuma bin ta kansu ba, domin kuwa ta gama dasu. Baki dayan su mamakin ta suke ji domin ita ɗaya ce kawai take abin da ta gadama, dukkan su suna karkashin inuwar Sultanate. "Yanzu Sultanate kenan ita Badi'atul Noor babu wanda ya isa da ita?" "Hmmm! Me zance tunda ta shigo rayuwar sa, shi kenan ai sai ta fita ta bar masarautar." Ta fada tana kallon Sultan. "A'a babu inda zata, ta zauna masarautar kawai zan duba maganar ta." Zaro idanu tayi tana faɗin. "Kamar ya? Ta bar Masarautar nan kawai" "mata ta ce, taya zan kore ta tabbas nima zan yi murabus." A tsorace Sultanate ta ce. " Akan dan wannan maganar ce zaka yi murabus?" "Na gaji ne Sultanate na gaji fitinar yau da ban na gobe daban ya ake so nayi? Don Allah ku bar ta ta huta domin hutunta shi ne hutuna " ya fada haka a sanyayye. " Shi kenan " ta mike ta bar falon cikin fushi. ......... Masarautar Kwara. A karni na sha uku, Masarautar ƙabilar yarbawa suka amshe ta, a hannun wasu kabilu, inda suka cigaba da da addinin gargajiya. A karni na sha hudu Mujaddadi Shehu Usmanu danfodiyo ya tura da wakilin shi Malam Abdul Aalim, inda yayi kira da azo a karbu musulunci. Duk da lokacin bai shiga cikin masarautar kwara ba, yana babban cibiyar masarautar da yake ibadan ne na da, a hankali tafiya da almajiranci ya kawo masarautar Kwara. Inda ya samu Sarkin da yake kai Afonja . Sam malam Abdul Aalim bai da burin raba Afonja da mulkin shi kasancewar ba mulki ya kawo shi ba, da'awa ce ta kawo shi, amma Afonja yaki sauraron shi, asalima sai ya shirya wata runduna na musamman suka yaƙi Shehun malamin,har ya bar yankin baki daya, shi da tsararun mutanen da suka amshi musulunci. Sai ya rubuta wasika izuwa Mujaddadi Shehu Usmanu danfodiyo. Sati uku a tsakanin sai ga sakon a yaki Afonja wanda tsabar kunya domin an ci kwara a lokacin da yaki, inda kabilu uku suka ci yaƙi. Saboda irin tarihin da ya ke da shi na musamman na Ilorin, na farko a matsayin Yarbawa daga cikin Daular Oyo, sannan a matsayinta na fulani mai mulkin Halifancin Sakkwato, tana da al’adar yin sarauta wadda ta kasance gauraya da al’adun gargajiya da aka samo daga bangarorin biyu. Duk lokacin da sarautar Masarautar (wadda ke hannun Fulani zuriyar Shehu Alimi) ta kasance babu kowa, wakilin kowace kwata a masarautar wato; Balogun Gambari (Hausa), Balogun Ajikobi (Yarabawa), Balogun Fulani (Fulani) da Balogun Alanamu (Yoruba) - tare da shugaban gidan sarautar Afonja, Mogaji Aare, da kuma babban hakiminsa mai suna Baba. Isale na Ilorin - a taru domin zabar sabon sarki tare da nada sabon sarki, bisa amincewar gwamnan jihar Kwara. Sannan an ba wa Balogun mafi dadewa sarautar Balogun hudu sarautar Balogun Agba, wanda hakan ya sa ya zama na biyu a kan Sarkin Ilorin. Dukkan Balogun na da gundumomi da suke gudanarwa a madadin sarki. Akwai kuma sarakunan gargajiya da kowanne ake kiransa Daudu (ko Hakimin Lardi). Suna aiki ne a matsayin hakimai masu wakiltar sarki a garuruwan dake fadin masarautar Ilorin kamar su Afon, Bode Saadu, Ipaye da Malete, da dai sauransu. Izuwa yau kabilu biyu suka taka rawan gani sosai a masarautar, Fulani da Hausawa. Masu mulki Gyara Sarakunan Masarautar Ilorin:[3] Fara Ƙarshen Mulki 1824 1842 Abdusalami dan Salih Alimi 1842 1860 Shita dan Salih Alimi Fulani suka rike wannan matsayin tun bayan rasuwar Malam Aalim, 1860 1868 Zubayro dan Abdusalami 1868 1891 Shita Aliyu dan Shittu 1891 1896 Moma dan Zubayru 1896 14 Janairu 1914 Sulaymanu dan Aliyu 1915 Nuwamba 1919 Shuaybu Bawa dan Zubayru 17 Fabrairu 1920 Yuni 1959 Abdulkadir dan Shuaybu Bawa Hausawa sune suke rike matsayin har zuwa lokacin da mulkin ya koma hannun yarbawa. 30 Yuni 1959 1992 Zulkarnayni Gambari dan Muhammadu Laofe Dan Bawa "Aiyelabowo V" 1992 Agusta 1995[4] Mallam Aliyu dan Abdulkadir 1995 Zuwa Yau Abdurrhman Dan Aliyu Sulu- Gambari. Wanda ya kasance bayarabe ne. Domin a samu daidaituwar mulki na zaman lafiya, yasan ya an samu auratayya a tsakanin su baki daya, bahaushe zai auri bayarabiya da bafulatana da Bahaushiya. Kafin ya kara da wata kabila idan ta mishi. Haka zalika. Sultanate ita Bahaushiya ce, mijin da ta aura kuma bayarabe ne, wacce sunanta Mansurah. Yaranta biyu ne kacal a duniya, ita ce mata ta biyu a wurin Sultan Aliyu Dan Abdullahi sulu gambari, uwargidan ta bafulatana ce, tana da Yara maza biyu mata biyu, sunan Aisha boddi ake kiranta, sai me bin Sultanate Tawakaltullah, wacce take da yara mata uku. Abdulsamad Dan Aliyu sulu gambari, sai Jamaluddin dan Aliyu sulu gambari. Sai Amrah dan Aliyu, sai Nana Asma'u dan Aliyu. Dakin Sultanate, akwai Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, akwai Warisah dan Aliyu. Dakin Tawakaltullah tana, Rufaidah dan Aliyu, Atikah dan Aliyu, da Batula dan Aliyu. Mata uku Dan Aliyu yayi a rayuwar shi, sannan bayan rasuwar shi aka bawa Abdulsamad mulki, wanda an bashi mulkin da sati daya ya rasu sakamakon sarar maciji. Yana auren Suhailah, yaransu uku Abdulrashid Abdulsamad Dan Aliyu, yana nan tantirin mara mutunci ne, kusan sa'an Muhammad dan Dawlat khatoon , sai kanin shi Abdulkarim. Shi kan yana Saudiya tun kafin rasuwar mahaifin su, sai kanwar su Sarah wacce kawa ce ga Ummu Mansurah. Warisah dan Aliyu, kawar Badi'atul Noor ce tun Yaranta. kuma suka taso a tare. Sai dai ita Allah bai bata haihuwa ba, inda ta auri Yayan Badi'atul Noor, ita kanta Badi'atul Noor su din jinin Shehun malamin nan Abdul Aalim sahili ne, mahaifinta jinin gidan ce yayinda mahaifiyar ta, ta kasance shuwa arab. Daga yankin borno. Su uku ne a cikin dakin su. Alhaji Khamal dan Umaru yana London Nigeria ambassador a can, sai Dawlat khatoon wacce take bin sa, sai Badi'atul Noor, da take bin Dawlat khatoon. Ita aka bawa Sultan Abdulrahman Dan Aliyu, zabin iyaye ne, ita kuma Badi'atul Noor tana da wanda take so wato Alhaji Marwan Muhammad Dan shitta. Soyayya suke me tab'a zuciya da ruhi, kowa a cikin masarautar da kewayenta yasan soyayyar Marwan da Badi'atul Noor, dan sune ake musu ikirarin Layla da majnoun, domin soyayyar tayi karfi da tasa idan daya na ciwo daya ma zai kwanta, ganin haka iyaye suka shiga al'amarin su. A lokacin Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari yana can ƙasar kalaba da matar shi, Dawlat khatoon da dansu Mahmud. Ga kuma wani cikin da take dauke da shi. Aka kira shi Yayan shi Abdulsamad Allah ya mishi rasuwa. Domin tsakanin Abdulsamad da mahaifin su sati biyu ne, yana zuwa gaisuwa ba tare da wani haufi ba, aka bashi gadon mulkin dan uwansa wanda Hajiya Suhailah da ta fito daga cikin ƙabilar Hausawa take fatan a bawa D'anta a lokacin, yaron kuma yana karami don haka aka bawa kanin mahaifin shi. Sati daya da bawa Abdurrhman Dan Aliyu sulu gambari mulki Allah yayiwa dan shi Muhammad rasuwa, inda aka tsinto gawar shi a cikin rijiyar masarautar. Mutuwar yaron ya tab'a kowa domin akwai shiga rai. Wata biyu da mutuwar shi, Dawlat khatoon ya fara nakuda, tun safe ake abu daya, domin ana da tabbacin cikin jikinta tagwaye zata haifa, sai da aka kwana aka wuni, kafin ta mahaifi yaran gawarwarki, awa biyu bayan nan sai gawarta aka samu. Tace ga garin ku, Sultan ya kadu ainun. Kwanaki arba'in da rasuwarta babu wani jan lokacin Mahaifin su Alhaji Abubakar Imam Aalim ya aurawa Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari Badi'atul Noor, ita kuma Warisah aka bawa Marwan. Kawayen biyu sun shiga kidima da tashin hankali. Musamman Badi'atul Noor da tayi ta suma tana farfaɗowa. Mahaifinta ko nace gidan su, tun bayan da mulki ya fita daga cikin gidan su, suka rike malunta sune suke jagorancin babban masalacin idi, sannan shi din babban alkaline daga kotun shara'ar musulunci. Haka aka kai Badi'atul Noor gidan mijinta. Tun daga nan yar matan nan ta shiga gujegujen bata zaman gidan, idan ta fita ta gudu sai tayi kwana uku ba asan inda take ba, ko a jikin Sultan asalima radadin mutuwar matarshi ya fiye mishi kome, haka suka share wata biyar, a lokacin da mahaifin yazo ne, yake tambayar ta cikin kunya da k'ame kame ya ce mishi ai yau kwananta biyu bata gida ta gudu. Kallon shi yayi kafin ya ce mishi. "In sha Allah bata kuma fita" daga haka ya fita. Kwana ɗaya a tsakanin sai gata ta dawo da kafarta. Amma kiyayyar da take mishi bata boye ba a gaban kowa nuna mishi take bata son shi. Da wannan yanayin har alaka me karfi na auratayya ya shiga tsakanin su. Duk yadda taso ta gudu ta gaza don dole ta hakura, shi kuwa Sultan tunda ya same ta, ya samawa kan shi nutsuwa da tsiwa da rashin mutunci tayi amma bai hana bawan Allah nan gyara mata zama da bulalan shi ba, kiyayyar tai nisa da ta fara cewa sai ta kashe shi abin da ya fara hada su da Sultanate kenan, domin da farko ganin babu jituwa a tsakanin su yasa baki daya ta zuba ta agefe. Ta shiga nima mishi yaran manyan mutane. A cikin rigimar Badi'atul Noor ta fara laulayi, tayi kuka tayi Allah ya isa tsakaninta da shi yafi kwando dubu. A haka har cikin ya isa haihuwa. Ta haifi Abubakar, watan Abubakar goma ta fara laulayi, babu yadda bata yi ba amma fir cikin ya zauna sai dai ta wahala don kanta. Tana haihuwarsa shi watan shi biyar ta samu cikin Rumaisah. Daga nan ta ajiye kayan yakinta. Haka tayi renon Rumaisah har aka haife ta. Rumaisah tana da shekara daya ta haifi Zakiyyah, daga nan tace ta gama haihuwa. Kuma wani abin burgewa yadda take kula da Yaran da shi kansa mijin ba karamin al'amari ba ne, ita kanta wani lokaci har dariyar kanta take yadda tayi ta kiyayya gashi ta haifa mishi yara har hudu, Zakiyyah na da shekara shida ta haifi Ummul Aymana, anan ma taci alwashin tayi auta, Shakaran Aymana uku sai ga cikin auta. Tasha wuya sosai domin shi aiki aka mata sannan aka rufe bakin mahaifan. Aka ajiye haihuwar itama ta guda. Yaranta shida uku mata uku maza, a lokacin Sultan ya kara mata biyu, Hajiya Badariyyah, sai Hajiya Mariyah, sai Hajiya Turai wacce take mugun kishin Sultanah karama. Akwai kiyayya me yawan gaske a tsakanin su. Domin basu ki su kashe Sultan ba. Warisah matar Marwan Muhammad Dan shitta, Kanwar Sultan. Yaranta uku mata. Hamdiya da Aneesah sai Ummul Mansurah, wacce ta ci sunan Sultanate. Bayan haihuwar Mansurah ne tayi hatsari, ta rasu. Dama ta roki Alhaji Marwan don Allah ko bayan ranta ne a bawa Badi'atul Noor rikon Mansurah. Bayan rasuwar ta kuwa ya bata Mansurah haka suka taso kai ɗaya da Aliyu domin tana da jikin girma. Tun lokacin hatsarin mahaifiyar su ta samu matsalar bata magana, haka yasa Abu turab shima baya magana, wanda da yana magana tar. Juyin duniyar nan Aliyu yaki magana dole aka saka su a special school na handicapped. Tun daga lokacin aka fara kaiwa Abubakar da Umar hari, a lokacin Alkali Abubakar ya bawa Sultan Abdulrahman Dan Aliyu shawaran a d'aga yaran daga cikin gidan a tura su London wurin Khamal. Haka suka tafi aka bar mata Abu turab. Sai dai me bayan tafiyar su, aka juyo kan Abu turab. Haka kawai yaron ya zama wani irin marajin magana, don ma Allah ya taimaka ita din ba kanwar lasa bace, bata wasa da ibada da sakaci da Addu'a, suna yi Allah ya a warware mata...... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza. [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: SANIN GAIBU...!! _Sai Allah_ ͲϴᏢ-ΝϴͲᏟᎻ 2023 *Mai_Dambu* Page:10 Last free pages Tunda aka dauke su Abubakar wanda sune suke kiran shi da Maina, tare da Umar wanda suke kiran shi da Saraki. Aka juya kan Abu turab, domin soyayyar da Sultanah da Sultan suke mishi ya dakushe na kowa, haka yayin sh mata, basu da wani burin da ya wuce suga farin cikin dan uwansu kuma autan su. Idan ka ga yana walwala yana tare da Rumaisah da Zakiyyah, Ummu Aymana kuwa dambe kawai basu yi domin ya masifar rena ta, irin na sako da sako, duk da ta bashi shekara goma. Ga Mansurah a gefen shi shakuwar su tun daga yarinta ne har girman su. Kuma abin da zai baka mamaki yadda ya iya magana da ita, haka ma Umminsu ta iya magana da ita. A hankali lokacin yayi ta tafiya, a gefe daya idan kika cire sakalci da shagwab'a tow kar ki kara kar ki rage Aliyu sulu gambari karshe ne, har tsiya Ummu Aymana take cewa. "kai dai ka ji kunya, kai shagwab'a matarka ya zata yi?" D'agawa Ummu Mansurah gira yake ya tambaye ta, "zaki iya da shagwab'a na?" Kunya yake saka ta jin kamar ta nutse. Haka yake babu ruwan shi da boye boye, ya taso cikin kyakkyawar tarbiyya ga kawaici da kamun kai uwa Uba zurfin nazari da zurfin ciki, haka yasa baki daya ya daura tunanin shi wurin karanta tsarin shari'a, yana gama secondary school, ya samu A.b.u zaria, a cikin hausawa yayi degree din shi na farko a fannin law. A lokacin Mansurah tana nata karatun ta a bangaren jarida, saboda ana ɗaukar masu disability, domin fassara abin da masu magana suke. Lokacin da ya gama jami'a suka tafi Umara da Ummin shi da Zakiyyah wacce take aiki da First bank na Illorin ɗin. Domin ita ta biya musu a cikin wata azumi suka tafi. Tunda suka isa idan suka yi ibada suka dawo gida daura kan shi yake akan cinyar Ummin shi kafaffun shi yana saman jikin Zakiyyah, idan Mansurah tana zuwa ta gansu. Ture kansa take ya fadi. Sai ta koma ta hau cinyar Ummin ta ce mishi da hannu. "Kai ko kunya baka ji, kazo ka wani haye cinya kamar baby, tow sauka" ta koma ta kwanta. Ita kanta Ummin su tana girmama soyayyar da suke yiwa juna. Bayan sun dawo aka yi musu baiko, domin an tura su service NYC inda aka turo mishi ya samu Sokoto. Kuma dama Kakar Badi'atul Noor uwar Babanta Yar gidan Sarautar Sokoto ce, da ita da Matar sarki musulmai y'ayan mata ne, shi Sokoto a wurin shi gida ne. Ana gobe zai bar illori a ranar an kwana an wuni ana zuba ruwa me yawan gaske. Don haka basu hadu da ita ba. Ita kuwa tana can wurin Sultanate akan lallai ta rabu da Aliyu Abu turab ta auri Abdulrashid, dama ba shiri suke da yaran gidan marigayi Abdulsamad ba, har Gara Abdulkarim suna shiri da shi ma ba cancan ba, Sarah kuwa kiri kiri suke fada domin tayi mata alkawarin sai ta auri Aliyu ko zata mutu. Don haka taki da ta gaji da magiyar da suke mata, ta turawa Aliyu sako. *Prince zo ka ɗauke ni na gaji don Allah* yana falon Ummi ya kwanta akan cinyar Rumaisah yana zuba shagwab'a domin tazo tunda mijinta baya gari. "Addah don Allah zaki kawo min visiting?" "Amma dai baka da kunya kato kawai saukar min a kafa." "Haba princess please Ummina saka baki" make bakin shi tayi tana faɗin " gidan ku, Ummin mu" tura baki yayi yana faɗin. "Oho dai sai kin kawo min ziyara sokoton...." Rike kirjin shi yayi ya tashi zaune yana haki, Ummu Aymana da ta shigo ta dauko goran ruwa ta mika mishi. Karba yayi ya sha rabin goran, sannan ya ajiye. "Auta ya dai?" Kallon wayar shi yayi yana haske. *Please ki kwana a can gobe sai ki fito da wuri* yasan idan ta gani zata mishi reply. "Baba karami meke damunka?" "Ba kome Ummi." Ya fada tare da nufar falon kasa ya dauki umbrella ya nufi bangaren su, bata nan kallon Zuwairah yayi ya ce mata." Baby bata dawo ba ne?" "Eh ranka shi dade" gaban shi yana faduwa ya fita domin ya dace ace ya je din amma bai je ba, tunda ya fita tsigar jikin shi yake tashi har ya nufi bangaren Sultanate. Ya same ta zaune tana shafa man zafi a gwiwar ta. Wayar ta ce tayi kara. "Waye?" "Tow ku gama kawai" sannan ta cillar da wayar. Tunda yayi sallama ta amsa bata kuma magana ba, asalima ko kallon inda yake bata kuma ba. Tsaki yayi zai juya ta ce mishi. "Kai dan iska waye kakewa tsaki" ganin kira yayi a wayar shi. Dubawa yayi yaga number Baby. Koda ya bi kiran wayar a kashe. "Ba ni da lokacin ki" ya fada can kasa. "Mara kunya wallahi ka min rashin kunya sai na saka Abdulrahman ya sake uwarka." Kallon wukar yanka tufa a gabanta, don haka ya dawo da sauri ya dauka. "Kai dan Ubanka me zaka yi da shi?" "Zan yanke harshen tsohuwa mara jin magana ne" sun tab'a haka da Abdulrashid ya mishi gatsali akan Idanunta abin ya faru, dauran yajin barkono yayi ya guntsa a bakin shi ya watsa mishi a fuskar shi, sannan ya ja zanin da aka daura kayan abinciin ya watsar da kayan abincin ya daure kan Abdulrashid yana me zuba mishi gargadi. "Kar ka kuma shiga harkata domin bani da kyau idan ka sake na kuma ganin kanwarka tawa Baby Iskancin sai na murde wuyar ka, zan nuna maka iskancin karya kake" tun daga ranar Sultanate ta shiga hankalin ta, domin tana mishi wulakanci da cin mutuncin bai tab'a kulata ba. "Kika ce me?" Ya tambaye kai tsaye. "Shin me ma nace na manta" jefa wukar yayi ya caki apple yana kallon ta. "Uwata matsayin ta daban haka ke matsayin ki daban, kar ki sake na kuma jin wata maganar b'atanci akan zinariyata" daga haka ya fita yana jin wani irin abu na yawo a jikin shi tabbas akwai wani fararren al'amari da yake ji zai faru ko ya faru. Haka ya wuce bangaren su. Sultanate kuwa sai da ta tsuge da kashi domin dan banza ya bata tsoro, babu abin da yake razana yan gidan baki daya kamar yadda Abu turab yake nuna musu kiyayya, duk wanda ya tab'a mishi uwa sai yaci uban sa. Haka yasa dayawan mutanen suke kallon Aliyu shi ne karfin Sultanah karama, domin idan babu shi a gefenta bata da wani karsashi. Abin da basu gane ba. Itace karfin shi domin idan babu ita a gefe bai cika shiga harkan kowa ba, sannan aduniyar shi ya tsani ka tab'a mishi ita shi yasa basu ga maciji da sauran matan. Domin ko lokacin da aka bashi guba ya ci idanun shi ya kuma budewa da rashin mutunci, amma a gaban Sultan ko Sultanah Badi'atul Noor ko yan uwan shi, mugun sangartacce ne. Goya shi ne kawai ba ayi. Amma baki daya al'amarin shi na sakaltattun yara ne. Kwanciya yayi da tunanin tura mata sako amma babu reply. Washi gari da sassafe ya wuce inda zasu tafi, bayan ya gama jiranta. Har ya bari garin babu labarin ta, wurin karfe goma na safe aka tsinci gawarta a bayan part din shi, bayan an keta mata alfarma anci zarafinta. Hankalin al'ummar masarautar ya tashi faruwar wannan al'amarin, yayinda wasu suka ce Aliyu Abu turab ne, wasu suka ce bashi ba, Sultanate kuwa ta kad'u da mutuwar yarinyar domin kaunar Warisah ya shafi Mansurah uwa Uba jikar ta takwaran ta, jikar da take so. Domin duk Yayunta sunyi auren Y'ay'an Badi'atul Noor ne, ita kuma da kanta taso haka domin kara dankon zumunci, ganin su take kamar aminiyarta dalilin da yasa take dauke kai akan Sultanate kenan. Hamdiyah tana auren Umar saraki, Aneesah tana auren Abubakar Maina, kuma dukkan su Allah ya albarkace su da zuri'a, Maina yaran shi biyu duk maza, sai Saraki shima mace da namiji, sun kwantar da hankalin su a can inda suke. Kuma suna zaune lafiya da soyayyar juna, wani abin burgewa duk shekara sau daya suke zuwa,.bata fasa musu addu'a da sadaka ba, domin tasan wayon ba shi ya ƙare su ba, Allah ne ya kare mata su. *** Yau sati biyu kenan da fara koyarwa, idan ya saka idanun shi akan Bimbi. Sosai yake lura da al'amarin ta, abu na farko da ya fara shine saya mata materials na karatun su, a cikin wannan yanayin sau uku Malam Aminu yana zuwa daukar ta, amma ya hana shi tafiya da ita. Yau Laraba ita kanta so take ta gudu makarantar domin ta lura da yadda Baffan su yake ta lekowa dakinsu yana kallonta. Tsoro ya saka ta shirya ko karyawan bata yi ba, haka bai wani dame shi ba, domin yayi alƙawarin daukar ta. Koda Inna Laminde ta fito ta samu ta tafi, shi kuma yana wurin dabobbin sa. "Laminde wai ba zaki gama abin karyawan nan ba ki sallame yara ba ne?" "To malam ai ta tafi ita kan Harirah zo ki dauka muku." Sake laggen hannun shi yayi ya sake sake tsaki, ya fita da sauri yana jin haushin ta. Koda ya isa ya samu ta shiga Makarantar, cafke hannunta yayi yana janta. "Wai kai Malam Aminu meye matsalar ka be? Ka bar yarinyar nan ta huta mana" "tunda ba yarku bace da sauki ai" wani malami da yake koyarwa a makarantar ya mishi magana, zai kuma magana Aliyu ya rike hannun shi yana cewa "kyale shi" haka ya ja hannunta ya tafi da ita. Murmushi Aliyu yayi domin ya samu labarin halin shi tsaf. Shi yasa shi kuma ya fito da na shi tsari. Daga makarantar gida ya wuce da ita ya tsaya a wurin hiran su, ya basu ajiyar ta. Sannan ya tafi gidan shi, yaje ya shirya tsaf. Sannan yazo ya tafi da ita. Mutumin dai be tsaya a ko ina ba, sai a Sokoto. Inda yayi ta binciken Office din NGO. Sai dai kash koda ya isa yan sanda suka yi ram da shi akan ya sato yar mutane zai yi safara da ita, ya ci duka sosai domin ana samu cases haka musamman da Dr Sharif Hamidu ya saka cewa duk wanda ba a yarda da shi ba, aka gan shi da Yara a kama shi, sun yi haka ne domin dakile miyagun ayyukan da ake yi. Sai da yayi kwana uku kafin aka nemi Yaran shi domin ya fadi sunan Zakaria, sub canza mishi kammani kan, sannan aka so shiga da case din kotu domin sun tabbatar da cewa sayar da ita yazo yi. Wannan abin ya saka shi jin haushin Bimbi domin gani yake she is a bad luck a rayuwar shi. Bayan an sallame shi, matar da ta kai Sa'ade gidanta ta kawo ta, yarinya a cikin kwana uku ta haɗa kumatai. A can Maikulki kuwa hankalin kowa ya tashi domin gani suke an sace su baki daya, Mai gari sai magana yake, dalilin maganar Aliyu ya tawo har sokoton, domin yana sane da kome. Kan wuri ya fara sauka ya huta, sannan ya kira Zakaria. Suka yi magana ya ce mishi. "Ka taimaka a maida ita gida, kayiwa Mama bayani, sauran kuma zan san yadda zan yi da shi, but ita din ta bar garin ya daina ganinta." "Mun gode sosai haka da kayi ma ka kyauta." "A'a kuyi hakuri da abin da aka mishi" "no need ya cancanci haka" kwana biyar a Sokoto ya koma gida, inda yayi karyan hatsari yayi, ya kuma umarci Zakaria da fadar haka. Bayan ya koma dakin shi Zakaria ya shiga dakin Innar su da Sa'ade. "Innar mu mun same ku lafiya?" "Lafiya lau wai da gaske hatsari yayi" "a'a" ya zauna ya gaya mata gaskiya, sannan ya kara bata labarin yadda Aliyu yazo har Office din su da maganar Sa'ade, sannan ya mika mata takardan makarantar ta. Kukan farin ciki Inna Laminde ta saka, domin abin ya mata dad'i, tayi ta saka mishi albarka. A gefen Aliyu kuwa so yake ayi ta ta kare. Ranar juma'a bayan an taso masallaci, ya tsare Malam Aminu cikin mutuntawa ya ce mishi. "Baban Sa'ade ashe kayi hatsari?" Ya fada yana haɗe rai. Kallon fuskar shi yayi baki daya sai ya kasa boyewa Aliyu gaskiya." Kai dai manta kawai yarinyar can ya ja min dukar tsayi lokacin da kuka ce na hakura da na hakura da duk haka bai taso ba." "Wacece kenan?" Aliyu ya tambaye shi. "Sa'ade ina ga farar kafa na haifa, yarinya ta sani asara da jin kunya da zan samu me sayar da ita zan sayar da ita tunda zargina ake" mamaki ya cika Aliyu, ya ce mishi" sai ka sayar da ita?" "Kwarai kuwa" "ka nimo shaida" "yawwa ga Malam Musa kalla can" "kima gaya masa zaka yi zaka sayar da ita?" "A'a karsana ta zance mishi" haka kuwa aka yi suna zuwa gaban Malam Musa ya ce mishi."na sayar da karsanata wa baturen binni" "nawa ka mata kudi?'" "kai nawa ka saya?" "Ka fada sai na nemi ragi idan xan iya" Malam Aminu ikon Allah. "Kai dan Bature, nawa zaka saye ta ban damu da ko nawa zaka bani ba, fata na kar na kuma ganin kafarta a gidana...." "Na saye ta dubu dari uku." "Ciniki ya fada" inji malam Musa. "Kar ka sake ta kuma dawowa nan idan kaso ka tafi da ita duniyar da ba zata iya dawowa ba, na sayar maka da ita.." "Malam Aminu ya kake abu kamar kana sayar da dan Mutum?" Malam Musa kalla ya tambaye shi, a firgice ya kalle shi, "a'a kasan saniyar da sabo zai yi yiwa ta saba da shi." "Aiho na zata wani abu ne dai." Nan ya ciro mishi tan dari biyar biyar guda shida ya mike. "Zan zo na dauka da safe gobe " "shi kenan " *** Kasancewar har yau ana bincike yasa bata wani samun isasshen barci sosai, yau tun magariba ta kwanta. Duk da taso ganawa da Sultan amma fir yaki bata damar ganin shi. Takaici yasa ta dawowa gida ta kwanta. Wurin karfe biyu na dare wayarta ya fara ringing lokacin tana wani irin mafarki, wai ga shi an danne Yaranta za a musu yankan rago, ita kuma an daure ta. Kokari take ta kunce daurin da aka mata amma ta kasa, kiran wayar ya farkar dabita bakinta dauke da salati. daukar wayar tayi ta ga Sarkin Kofa. Karawa tayi a kunnenta. "Hello Hello Hello!!! Sultanah Badi'atul Noor, ki kare yaranki idan ta kama ki tara su a gaban ki ne duk daya, ke dai ki kasance garkuwa a gare su, domin Yakin naki ne babu me taya ki sai Allah, da maku... Ahaaaaaa" ya fasa ihu da karfi ya fadi kasa. tana ji"hello sarkin kofa" "idan kin samu hali ki kare Yaranki, kar ki yarda da kowa domin kowani mutum za a iya sayan shi ya ga bayan ki. Do....." Karan karfe da buguwar abu taji... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan. +234 8130269641 +234 813 731 1900 +234 906 346 7258 +227 84 50 64 76 Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar Top-notch season 2 2023 [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan. +234 8130269641 +234 813 731 1900 +234 906 346 7258 +227 84 50 64 76 Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar Top-notch season 2 2023. *Page Sir Ahmadu Bello* A firgice ta cire wayar a kunnenta, idan hankalin ta yayi dubu to ya tashi a wannan daren da sauri ta dauko hijabinta na sallah, ta fita da gudu, gudu ba na wasa ba don m Allah ya taimaka bata da nauyin jiki, jin motsinta yasa sauran masu kula da harkokin ɓangaren ta suka fito suma suka rufa mata bayan ta. Har bangaren Sultan suka nufa, suka yi ta buga kofar bangaren dakyar ya fito ya bada izinin a bude mata. Yasanta ya kuma san halinta tun kuruciya kaifi daya ce, bata karya bata munafinci bata kuma gulma, gaskiya ce zata fadeta sai dai ka mutu. Amma yau ya ganta a gabansa a cikin yanayin firgici. "Lafiya" rike hannun shi tayi tare da sau jikinta ta zube akan gwiwar ta, tana me fashewa da kuka, ganin yadda take kuka yasa shi, zama yana fuskartatta. "Badi'atul Noor!" Ya kira sunan ta, in low voice tare da riko hannunta, "meke faruwa?" Dakyar ta iya hàdiye kukan ta, ta bude baki zata yi magana aka fara buga tambura. Kura mata idanu yayi. "Abin da zaki fada min yana da alaka da buga tamburan da ake ?" Hawaye ne ya zubo mata da mugun gudu. "Yarana Abdurrhman!" Kallonta yayi sosai domin shi dai bai tab'a jin ta kira sunan shi kai tsaye haka ba, sai yau. "Mene ne ya faru?" "An kashe Sarkin kofa, kafin su kashe shi ya kira ni ya ce na kula da Yarana." Ta fada muryanta yana rawa. Tab'e baki yayi yana faɗin."kuma sai ki tawo min kina kuka?" Da sauri ta kalle shi cike da mamaki, "Abd....!" "Kin ga in dai saboda Aliyu kike wannan abin tow ki daina, ki jira sakamakon abin da zai biyo baya kawai zaki iya tafiya" ya juya zai koma sama. "Zan tsaya musu, zan tsaya musu nace, amma ka sani ba zan tab'a yafe maka ba, domin na zo ina jin zafi a madadin ka zama kankaran da zai saya ni jin sanyi sai ka zama ruwan zafi mafi zafi a rayuwata." Ta fashe da kuka. "Me yasa ne? Me yasa baka damu da abin da zai je ya zk ne? Ka sake min ragamar kula da rayuwar Yarana baki daya, meye na maka? Ehe gaya min meye na maka? Ko don yanzu babu abin da zaka mora a jikina yasa nake wulakanta Ni? Nace ko dan babu abin da zai dauke maka gajiyar ka ke cin zarafina?" "Badi'atul Noor" "meye Abdulrahman? Nace meye?" Ta tambaye shi tana kallon shi, baki daya jikin shi yayi sanyi shi ba haka yake nufi da ita ba wallahi. "Kije gobe zamu yi magana" "idan ka so kar ka nime ni, in sha Allah ba zan kuma maka magana akan halin da Yarana suke ciki ba." Haka ta juya zata fita yana kallonta, har ta isa bakin kofar ta juya tana kallon shi. "ka rubuta ka ajiye na gama kuka na, daga ranar da wani abu ya faru, sai na kashe ka." Yadda tayi maganan da wani irin confidence yasa shi shan jinin jikin shi tabbas ran yan mata ya b'aci, yana tsaye Sarkin fada ya shigo tare da zubewa a kasa, yana faɗin. "Allah ya baka nasara, me Fulani da Hausawa, an samu gawar Bilyaminu a wajen masarautar nan" "a kira masu bincike su duba shi." Ya juya ya haura sama, bai shiga dakin da Badariyyah take ba, sai Safa da Marwa yake alamar yana cikin damuwa ainun, ya hango kiyayyar shi sabo fil a cikin Idanunta, ya hango kin shi amma bai hango mutuwarsa a hannun ta yake ba, domin ya san ta kai matakin da ba zata iya rayuwa babu yaranta ba. Har garin Allah ya waye babu wanda ya rintsa daga cikin gidan baki daya domin ko yan ba ruwana tsoro ta hana su barci. Ita kanta Hajiya Suhailah tattara Abdulrashid tayi ta kintsa shi a falon, dama Abdulkarim tun bayan mutuwar Mansurah ya bar garin yanzu ga shi an kashe Kabiru ga Gajiye bata da lafiya ko magana bata yi. Yanzu kuma ga Sarkin Kofa anya babu wanda yake son ganin bayan shi.? Wannan shi ne tambayar da yayiwa kansa. Bayan an gama bincike aka yiwa Sarkin kofa jana'izar shi. Kafin hantsi Zakiyyah da Rumaisah tare da Ummu Aymana sun zo gidan, ganin yadda Mahaifiyar su, take cikin damuwa yasa Rumaisah ta dauke wayar ta, ta kashe domin har lokacin kiran layin Abuturab take ko zai dauka. Amma wayar a kashe, dake Aymana nurse ce babba Allah ta mata da sunan na zazzaɓi ne. Take barci yayi gaba da ita domin naaa barci ne, tunda suka iso suka nufi bangaren mahaifin su, dake yana shiri sosai da Yaran shi mata, har waɗancan ƙananan yaran. Bayan sun mishi gaisuwa suka zauna suna dan tab'a hira, gyara murya yayi yana faɗin. "Ku kula da mahaifiyar ku, domin tana cikin damuwa " Da wannan suka fito daga wurin shi, suna zauna suka lura da bata taba barci ba, sai dai lokaci zuwa lokaci tana zubda hawaye, allurar barci suka mata, duk da abokan zamanta basu san halin da take ciki ba, amma kuma suna farin ciki da halin da take ciki idan ka cire Hajiya Turai da tafito tana faɗin. "Duk zurfin cikin mutum da iya takun shi karya ta kare mishi,." Domin har harabar Sultanah karama ta isa tana habaici. Barcin awa uku tayi ta farka daidai lokacin da Maina ya kirata. Zata dauki wayar Rumaisah ta dauka tana kallon fuskar ta. "Hammayo" "Na'am ya sebo? Ashe abin da ya faru kenan bayan barin Bamanga gida?" "Eh wallahi, al'amarin yayi tsauriwa Ummin mu, ina ga." Mikewa tayi tana barin dakin yan uwan suka bita da idanu, lumshe idanunta Badi'atul Noor tayi, domin bata da karfi a jikinta "Ummin mu ko zaki watsa ruwa ne?" "Abu Turab ya kira?" "A'a Hammayo ne ya kira" gyada kai tayi tana kallon kofar. Da taimakon Zakiyyah ta shiga ban dakin Ummu Aymana ta shiga kintsa dakin kafin ta fito. A ban dakin kallon Zakiyyah tayi tana faɗin. "Cika min ruwan." "Tow" ta fada tana cika mata ruwan, sai da ta ajiye mata kome zata fita ta ce mata. "Ki kira min Abu Turab" "tow zan kira shi" A falon sama na farko ta shiga ta zauna tana waya da Maina. "Hammayo ina ga ka shirya mata zuwa wurin ku, kai da Saraki haka ne kawai zai saka ta samu nutsuwa a ranta don Allah" "shi kenan, ku shirya nan da wata sati sai ta zo, amma why not mu haɗu a Umra zai fi nan, domin a can ibada zai rage mata damuwa, nan kuma Zulimi zai kara mata zama a nan din" "kuma haka ne, in sha Allah zan kira ka idan kome ya amma kuma yaushe ta dawo ko sati Uku ba ayi ba, sai dai tazo wurin ku kawai" "kuma gaskiya ne ba damuwa tazo zan gayawa Saraki, sannan anya babu wani abu da yake faruwa?" "A'a domin dai Dad bai gaya mana kome ba, amma ita na fuskanci akwai damuwa a ranta." "Tow Allah ya kyauta" "Amin Ya Allah" ya kashe wayar sai ga kiran Abu turab, "Auta" "Adda ina Jasrah?" "Lafiyan su lau." "Ina Ummina?" Murmushn karfin hali tayi tana faɗin."tana wanka an jima ka kira" "addaaaaaaaah! Ku haɗa ni da Ummu Mansurah please" "ka jira Ummi" ta kashe wayar, ta wuce zata fita haduwa tayi da Zuwairah tana wucewa zata kai kayan abinci dakin Ummin. "Kawo na kai." "Ayya Uwar ɗakina bari naga Ummin mu mana" "tow shi kenan" haka Rumaisah ta shiga gaba Zuwairah tana bin bayanta har zuwa dakin, ajiye tiren tayi tana gaishe su. "lafiya lau." "Ina Ummin?" "Yanzu zata fito" "tow Allah ya fito da ita lafiya" tana zaune a wurin sai ga Ummin ta fito,kallon Zuwairah tayi sannan ta ce mata. "Zuwairah" "Na'am Ummin mu, Sultanah! Ya jikinki? " "Da sauki" ta wuce closet dinta, ta zaɓi kayanta ta zauna tana shafa mai maganar Sarkin kofa ya dawo mata a rai. *Kada ki yarda da kowa! Kare Yaranki" zura doguwar riga Sweden cotton fabric lacce ta saka, dan kwalin yana hannunta ta fito. Ta zubawa Yaranta idanu, "kun tab'a wani abu daga ne a cikin abincin nan?" "A'a bamu tab'a kome ba" juyawa tayi ta koma sai da ta shirya sannan ta fito daga cikin dakin fuskarta tsam zaka iya rantsewa bata da wani damuwa a rayuwar ta. "Ummin mu kin fito? Ya jikin naki?" "Alhamdulillahi da sauki sosai." Zama tayi a gaban Abincin, ta kalli azurfan hannunta yayi duhu. "Zakiyyah cire min sarkan wuyar ki" cirewa tayi ta mika mata har da kwad'on, ta jefa cikin flask na tea ɗin. Sai d ya jima ta juye tea ɗin a cikin cups din wurin. Sai da tabi abincin baki daya ta jefa sarkan, ganin kalar shi bai sauya ba yasa ta kalle su. "zan baku shawara a matsayina na mahaifiyar ku, kuma kawar ku." Kallon su tayi ganin yadda suka tsare ta da idanu bata san lokacin da ta sake murmushin dole ba, tana faɗin. "Sannun ku matsorata sai kace nace ga dodo. Abin da zan gaya muku shi ne, ku nisanta kanku daga tara masu taya ku zama. Ku kula sosai, ku saka idanu domin akwai wani al'amari da naso." "Akan me zaki tara min yara kina razana min su da shirmen ki na banza?" Ya tambaye ta yana shigowa cikin dakin. Tura baki tayi tana faɗin"akan me ba zan gaya musu gaskiya ba, ko an ce maka kowa hakuri yake da shiri irinka? Ko ance maka kowa irinka ne" a hankali Rumaisah da take babba a cikin su ta mike. "Zauna wato kece kika d'agawa Maina hankali ko?" "A'a Dad halin da Ummin mu take ciki yasa nayi tunanin ta koma wurin shi " juyawa yayi yana kallon Badi'atul Noor. "Ke" d'ago fararren idanunta tayi ta zuba mishi fess, wani abu ta ji ya tsaya mata a wuyarta. "Babu inda zaki tafi, fisabilillahi me yasa kike kin min haka? Kin fini son Ƴaran ne?" Wani dauke kai tayi tana kurban shayi, "Allah ya huci zuciyar ka" ta fada a hankali, tana sassauta fushinta. Juya harshe yayi shi da Rumaisah suka shiga yin fulatanci, tana jin su, amma bata da niyyar shiga maganar. "Batun zuwan ta Ingila na soke" d'ago kai tayi tana kallon Rumaisah. "When aka yi shirin tafiya Ingila bani da labari?" Tambaye su. "Ummi wai mun ga stresst yayi miki yawa yasa muka yi decided ki tafi can ki huta." Kasa kasa ta kalle shi tayi kwafa,jan yaran sa yayi da hira domin yasan halinta tsaf ta wanke shi ba abu me wuya ba ne, shi kansa yasan kaf cikin matan shi zai yi wuya a samu biyunta domin ba ruwanta ko waye kai, kana mata ba daidai ba, zata magana sannan san jiya bata rai, amma ba haka yana nufin ba zai iya tunkarar ta domin rarrashi ba ne. Ko yanzu da ya zo ne domin ya bata baki amma yadda yaga fuskar ta yasa shi shanye duk abin da yazo da shi. *** Sokoto "Ikon Allah Sophia ce ta girma haka? When haduwar bata kai haka ba." Inji Hajiya Dawlah, dariya Uwar yarinyar tayi Hajiya Nazirah mata ga tsohon IG na yan sanda, ta ce. "Gata nan ai jikin girma ne da ita, aji ta biyu a Abti tana karanta environmental." "Masha Allah, Kice muna da duba gari kenan " "Ai fa gata nan, ya jikin Abdul da fatan an yi nasarar aikin shi da aka mishi." Jim tayi kafin ta ajiye kofin hannunta ta ce." eh tow Alhamdulillahi tunda sun bashi hutu kamar yadda naso yayi aure sun ce sai sun mishi aikin karshe tun ku, amma har ga Allah ina son yayi aure." "Gaskiya ayi hakuri tukun ya samu lafiya ai kome dan lafiya ne. Ya batun shegiyar kishiyar ki?" "Tsinanniya dai tunda ta raba ni da mijina da Abdul din ba, sun zaɓe ta ta musu asiri" ta fadi maganar a raunane. "Allah ya saka miki" sun jima suna daukar alhakin Aunty Faridah. "Assalamu alaikum, sannun ku da gida Hajiya " ya fada yana wucewa dakin shi. "Abdul baka ga bakinsa ba ce, Hajiya Nazirah ce makociyar mu na London " a fisge ya ce mata "ai sannu da zuwa ya wuce" abin ya b'atawa Hajiya Daulah rai kamarta danta yaga kawar ta na arzikn ya mata kallon hadarin kaji. Jinjina kai tayi ta ce "ina zuwa Hajiya Nazirah " ta bi bayan sá, yana zaune yana bude wardrobe din shi, dama can mantuwa yayi ganin yadda ta banko kofar yasa shi d'ago kai da sauri. "Me kake nufi? Ta maka kama da yar tasha ce?" "Hajiya don Allah kiyi hakuri" ya fada domin ya dakatar da jarabarta. "Abdul Hakim" kamar zai fasa ihu ya kalle ta. "Don Allah kiyi hakuri zan dauki files ne na manta." "Wuce muje ka bata hakuri" "Toh Hajiya" ya bar binciken ya nufi waje, haka suka fito ya cewa Hajiya Nazirah. "Kiyi hakuri." "Laaa ba dai fada kika mishi ba, ai da alamu sauri yake." "Koma mene ne ba zan dauki renin hankali ba." Ta gama cika bakinta ya bar su a wurin. "Banga Afiyyah" "suna da test ai bata gida" juyawa yayi abin sa bai kuma bin ta kan su ba."Don Allah ki turo min Sophia mana, ina son su hadu da su Afiyyah" "tow ba kome zata zo dake a can abuja take wurin kanwata" "don Allah ki turo min ita su saba da Yaran nan" " in sha Allah zan turo ta" motsin Abdul yasa su juyawa suja gan shi ya waya a hankali, kafin ya musu sallama ya bar gidan. "Gaskiya Abdulhakim ya girma yana bukatar iyali amma a ce magidanci irin sa babu mace ai bai dace ba, gaskiya ki tashi a tsaye domin haka bai dace ba" cikin yanayin jimami Hajiya Daulah ta ce mata" ya zanyi tow? Kowa ya juya min baya akan sai dai a bi Shawaran likita" "likita Allah ne? Babu abin da zasu iya idan zaki nima mishi mace wacce zata kula da shi amma abar shi babu mace akwai damuwa." Ai kamar an sosa mata inda yake mata kaikayi ta ce."ya zanyi? Baki daya sun ki amincewa na nima mishi aure, sannan shima har yau yaki maganar auren sai na kawo maganar zai fara kauce kauce. Wallahi na rasa yadda zan yi anya ba hannu aka saka mishi ba?" Kallon juna suka yi baki a bude kafin suka ce. "Tabbas biri yayi kama da mutum."..... African Queen products Sabulun matsi Garin matsi Humra Turaren wuta Maganin Infection Ga number wayata...08130269641 [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan. +234 8130269641 +234 813 731 1900 +234 906 346 7258 +227 84 50 64 76 Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar Top-notch season 2 2023. *Page Sir Ahmadu Bello* A firgice ta cire wayar a kunnenta, idan hankalin ta yayi dubu to ya tashi a wannan daren da sauri ta dauko hijabinta na sallah, ta fita da gudu, gudu ba na wasa ba don m Allah ya taimaka bata da nauyin jiki, jin motsinta yasa sauran masu kula da harkokin ɓangaren ta suka fito suma suka rufa mata bayan ta. Har bangaren Sultan suka nufa, suka yi ta buga kofar bangaren dakyar ya fito ya bada izinin a bude mata. Yasanta ya kuma san halinta tun kuruciya kaifi daya ce, bata karya bata munafinci bata kuma gulma, gaskiya ce zata fadeta sai dai ka mutu. Amma yau ya ganta a gabansa a cikin yanayin firgici. "Lafiya" rike hannun shi tayi tare da sau jikinta ta zube akan gwiwar ta, tana me fashewa da kuka, ganin yadda take kuka yasa shi, zama yana fuskartatta. "Badi'atul Noor!" Ya kira sunan ta, in low voice tare da riko hannunta, "meke faruwa?" Dakyar ta iya hàdiye kukan ta, ta bude baki zata yi magana aka fara buga tambura. Kura mata idanu yayi. "Abin da zaki fada min yana da alaka da buga tamburan da ake ?" Hawaye ne ya zubo mata da mugun gudu. "Yarana Abdurrhman!" Kallonta yayi sosai domin shi dai bai tab'a jin ta kira sunan shi kai tsaye haka ba, sai yau. "Mene ne ya faru?" "An kashe Sarkin kofa, kafin su kashe shi ya kira ni ya ce na kula da Yarana." Ta fada muryanta yana rawa. Tab'e baki yayi yana faɗin."kuma sai ki tawo min kina kuka?" Da sauri ta kalle shi cike da mamaki, "Abd....!" "Kin ga in dai saboda Aliyu kike wannan abin tow ki daina, ki jira sakamakon abin da zai biyo baya kawai zaki iya tafiya" ya juya zai koma sama. "Zan tsaya musu, zan tsaya musu nace, amma ka sani ba zan tab'a yafe maka ba, domin na zo ina jin zafi a madadin ka zama kankaran da zai saya ni jin sanyi sai ka zama ruwan zafi mafi zafi a rayuwata." Ta fashe da kuka. "Me yasa ne? Me yasa baka damu da abin da zai je ya zk ne? Ka sake min ragamar kula da rayuwar Yarana baki daya, meye na maka? Ehe gaya min meye na maka? Ko don yanzu babu abin da zaka mora a jikina yasa nake wulakanta Ni? Nace ko dan babu abin da zai dauke maka gajiyar ka ke cin zarafina?" "Badi'atul Noor" "meye Abdulrahman? Nace meye?" Ta tambaye shi tana kallon shi, baki daya jikin shi yayi sanyi shi ba haka yake nufi da ita ba wallahi. "Kije gobe zamu yi magana" "idan ka so kar ka nime ni, in sha Allah ba zan kuma maka magana akan halin da Yarana suke ciki ba." Haka ta juya zata fita yana kallonta, har ta isa bakin kofar ta juya tana kallon shi. "ka rubuta ka ajiye na gama kuka na, daga ranar da wani abu ya faru, sai na kashe ka." Yadda tayi maganan da wani irin confidence yasa shi shan jinin jikin shi tabbas ran yan mata ya b'aci, yana tsaye Sarkin fada ya shigo tare da zubewa a kasa, yana faɗin. "Allah ya baka nasara, me Fulani da Hausawa, an samu gawar Bilyaminu a wajen masarautar nan" "a kira masu bincike su duba shi." Ya juya ya haura sama, bai shiga dakin da Badariyyah take ba, sai Safa da Marwa yake alamar yana cikin damuwa ainun, ya hango kiyayyar shi sabo fil a cikin Idanunta, ya hango kin shi amma bai hango mutuwarsa a hannun ta yake ba, domin ya san ta kai matakin da ba zata iya rayuwa babu yaranta ba. Har garin Allah ya waye babu wanda ya rintsa daga cikin gidan baki daya domin ko yan ba ruwana tsoro ta hana su barci. Ita kanta Hajiya Suhailah tattara Abdulrashid tayi ta kintsa shi a falon, dama Abdulkarim tun bayan mutuwar Mansurah ya bar garin yanzu ga shi an kashe Kabiru ga Gajiye bata da lafiya ko magana bata yi. Yanzu kuma ga Sarkin Kofa anya babu wanda yake son ganin bayan shi.? Wannan shi ne tambayar da yayiwa kansa. Bayan an gama bincike aka yiwa Sarkin kofa jana'izar shi. Kafin hantsi Zakiyyah da Rumaisah tare da Ummu Aymana sun zo gidan, ganin yadda Mahaifiyar su, take cikin damuwa yasa Rumaisah ta dauke wayar ta, ta kashe domin har lokacin kiran layin Abuturab take ko zai dauka. Amma wayar a kashe, dake Aymana nurse ce babba Allah ta mata da sunan na zazzaɓi ne. Take barci yayi gaba da ita domin naaa barci ne, tunda suka iso suka nufi bangaren mahaifin su, dake yana shiri sosai da Yaran shi mata, har waɗancan ƙananan yaran. Bayan sun mishi gaisuwa suka zauna suna dan tab'a hira, gyara murya yayi yana faɗin. "Ku kula da mahaifiyar ku, domin tana cikin damuwa " Da wannan suka fito daga wurin shi, suna zauna suka lura da bata taba barci ba, sai dai lokaci zuwa lokaci tana zubda hawaye, allurar barci suka mata, duk da abokan zamanta basu san halin da take ciki ba, amma kuma suna farin ciki da halin da take ciki idan ka cire Hajiya Turai da tafito tana faɗin. "Duk zurfin cikin mutum da iya takun shi karya ta kare mishi,." Domin har harabar Sultanah karama ta isa tana habaici. Barcin awa uku tayi ta farka daidai lokacin da Maina ya kirata. Zata dauki wayar Rumaisah ta dauka tana kallon fuskar ta. "Hammayo" "Na'am ya sebo? Ashe abin da ya faru kenan bayan barin Bamanga gida?" "Eh wallahi, al'amarin yayi tsauriwa Ummin mu, ina ga." Mikewa tayi tana barin dakin yan uwan suka bita da idanu, lumshe idanunta Badi'atul Noor tayi, domin bata da karfi a jikinta "Ummin mu ko zaki watsa ruwa ne?" "Abu Turab ya kira?" "A'a Hammayo ne ya kira" gyada kai tayi tana kallon kofar. Da taimakon Zakiyyah ta shiga ban dakin Ummu Aymana ta shiga kintsa dakin kafin ta fito. A ban dakin kallon Zakiyyah tayi tana faɗin. "Cika min ruwan." "Tow" ta fada tana cika mata ruwan, sai da ta ajiye mata kome zata fita ta ce mata. "Ki kira min Abu Turab" "tow zan kira shi" A falon sama na farko ta shiga ta zauna tana waya da Maina. "Hammayo ina ga ka shirya mata zuwa wurin ku, kai da Saraki haka ne kawai zai saka ta samu nutsuwa a ranta don Allah" "shi kenan, ku shirya nan da wata sati sai ta zo, amma why not mu haɗu a Umra zai fi nan, domin a can ibada zai rage mata damuwa, nan kuma Zulimi zai kara mata zama a nan din" "kuma haka ne, in sha Allah zan kira ka idan kome ya amma kuma yaushe ta dawo ko sati Uku ba ayi ba, sai dai tazo wurin ku kawai" "kuma gaskiya ne ba damuwa tazo zan gayawa Saraki, sannan anya babu wani abu da yake faruwa?" "A'a domin dai Dad bai gaya mana kome ba, amma ita na fuskanci akwai damuwa a ranta." "Tow Allah ya kyauta" "Amin Ya Allah" ya kashe wayar sai ga kiran Abu turab, "Auta" "Adda ina Jasrah?" "Lafiyan su lau." "Ina Ummina?" Murmushn karfin hali tayi tana faɗin."tana wanka an jima ka kira" "addaaaaaaaah! Ku haɗa ni da Ummu Mansurah please" "ka jira Ummi" ta kashe wayar, ta wuce zata fita haduwa tayi da Zuwairah tana wucewa zata kai kayan abinci dakin Ummin. "Kawo na kai." "Ayya Uwar ɗakina bari naga Ummin mu mana" "tow shi kenan" haka Rumaisah ta shiga gaba Zuwairah tana bin bayanta har zuwa dakin, ajiye tiren tayi tana gaishe su. "lafiya lau." "Ina Ummin?" "Yanzu zata fito" "tow Allah ya fito da ita lafiya" tana zaune a wurin sai ga Ummin ta fito,kallon Zuwairah tayi sannan ta ce mata. "Zuwairah" "Na'am Ummin mu, Sultanah! Ya jikinki? " "Da sauki" ta wuce closet dinta, ta zaɓi kayanta ta zauna tana shafa mai maganar Sarkin kofa ya dawo mata a rai. *Kada ki yarda da kowa! Kare Yaranki" zura doguwar riga Sweden cotton fabric lacce ta saka, dan kwalin yana hannunta ta fito. Ta zubawa Yaranta idanu, "kun tab'a wani abu daga ne a cikin abincin nan?" "A'a bamu tab'a kome ba" juyawa tayi ta koma sai da ta shirya sannan ta fito daga cikin dakin fuskarta tsam zaka iya rantsewa bata da wani damuwa a rayuwar ta. "Ummin mu kin fito? Ya jikin naki?" "Alhamdulillahi da sauki sosai." Zama tayi a gaban Abincin, ta kalli azurfan hannunta yayi duhu. "Zakiyyah cire min sarkan wuyar ki" cirewa tayi ta mika mata har da kwad'on, ta jefa cikin flask na tea ɗin. Sai d ya jima ta juye tea ɗin a cikin cups din wurin. Sai da tabi abincin baki daya ta jefa sarkan, ganin kalar shi bai sauya ba yasa ta kalle su. "zan baku shawara a matsayina na mahaifiyar ku, kuma kawar ku." Kallon su tayi ganin yadda suka tsare ta da idanu bata san lokacin da ta sake murmushin dole ba, tana faɗin. "Sannun ku matsorata sai kace nace ga dodo. Abin da zan gaya muku shi ne, ku nisanta kanku daga tara masu taya ku zama. Ku kula sosai, ku saka idanu domin akwai wani al'amari da naso." "Akan me zaki tara min yara kina razana min su da shirmen ki na banza?" Ya tambaye ta yana shigowa cikin dakin. Tura baki tayi tana faɗin"akan me ba zan gaya musu gaskiya ba, ko an ce maka kowa hakuri yake da shiri irinka? Ko ance maka kowa irinka ne" a hankali Rumaisah da take babba a cikin su ta mike. "Zauna wato kece kika d'agawa Maina hankali ko?" "A'a Dad halin da Ummin mu take ciki yasa nayi tunanin ta koma wurin shi " juyawa yayi yana kallon Badi'atul Noor. "Ke" d'ago fararren idanunta tayi ta zuba mishi fess, wani abu ta ji ya tsaya mata a wuyarta. "Babu inda zaki tafi, fisabilillahi me yasa kike kin min haka? Kin fini son Ƴaran ne?" Wani dauke kai tayi tana kurban shayi, "Allah ya huci zuciyar ka" ta fada a hankali, tana sassauta fushinta. Juya harshe yayi shi da Rumaisah suka shiga yin fulatanci, tana jin su, amma bata da niyyar shiga maganar. "Batun zuwan ta Ingila na soke" d'ago kai tayi tana kallon Rumaisah. "When aka yi shirin tafiya Ingila bani da labari?" Tambaye su. "Ummi wai mun ga stresst yayi miki yawa yasa muka yi decided ki tafi can ki huta." Kasa kasa ta kalle shi tayi kwafa,jan yaran sa yayi da hira domin yasan halinta tsaf ta wanke shi ba abu me wuya ba ne, shi kansa yasan kaf cikin matan shi zai yi wuya a samu biyunta domin ba ruwanta ko waye kai, kana mata ba daidai ba, zata magana sannan san jiya bata rai, amma ba haka yana nufin ba zai iya tunkarar ta domin rarrashi ba ne. Ko yanzu da ya zo ne domin ya bata baki amma yadda yaga fuskar ta yasa shi shanye duk abin da yazo da shi. *** Sokoto "Ikon Allah Sophia ce ta girma haka? When haduwar bata kai haka ba." Inji Hajiya Dawlah, dariya Uwar yarinyar tayi Hajiya Nazirah mata ga tsohon IG na yan sanda, ta ce. "Gata nan ai jikin girma ne da ita, aji ta biyu a Abti tana karanta environmental." "Masha Allah, Kice muna da duba gari kenan " "Ai fa gata nan, ya jikin Abdul da fatan an yi nasarar aikin shi da aka mishi." Jim tayi kafin ta ajiye kofin hannunta ta ce." eh tow Alhamdulillahi tunda sun bashi hutu kamar yadda naso yayi aure sun ce sai sun mishi aikin karshe tun ku, amma har ga Allah ina son yayi aure." "Gaskiya ayi hakuri tukun ya samu lafiya ai kome dan lafiya ne. Ya batun shegiyar kishiyar ki?" "Tsinanniya dai tunda ta raba ni da mijina da Abdul din ba, sun zaɓe ta ta musu asiri" ta fadi maganar a raunane. "Allah ya saka miki" sun jima suna daukar alhakin Aunty Faridah. "Assalamu alaikum, sannun ku da gida Hajiya " ya fada yana wucewa dakin shi. "Abdul baka ga bakinsa ba ce, Hajiya Nazirah ce makociyar mu na London " a fisge ya ce mata "ai sannu da zuwa ya wuce" abin ya b'atawa Hajiya Daulah rai kamarta danta yaga kawar ta na arzikn ya mata kallon hadarin kaji. Jinjina kai tayi ta ce "ina zuwa Hajiya Nazirah " ta bi bayan sá, yana zaune yana bude wardrobe din shi, dama can mantuwa yayi ganin yadda ta banko kofar yasa shi d'ago kai da sauri. "Me kake nufi? Ta maka kama da yar tasha ce?" "Hajiya don Allah kiyi hakuri" ya fada domin ya dakatar da jarabarta. "Abdul Hakim" kamar zai fasa ihu ya kalle ta. "Don Allah kiyi hakuri zan dauki files ne na manta." "Wuce muje ka bata hakuri" "Toh Hajiya" ya bar binciken ya nufi waje, haka suka fito ya cewa Hajiya Nazirah. "Kiyi hakuri." "Laaa ba dai fada kika mishi ba, ai da alamu sauri yake." "Koma mene ne ba zan dauki renin hankali ba." Ta gama cika bakinta ya bar su a wurin. "Banga Afiyyah" "suna da test ai bata gida" juyawa yayi abin sa bai kuma bin ta kan su ba."Don Allah ki turo min Sophia mana, ina son su hadu da su Afiyyah" "tow ba kome zata zo dake a can abuja take wurin kanwata" "don Allah ki turo min ita su saba da Yaran nan" " in sha Allah zan turo ta" motsin Abdul yasa su juyawa suja gan shi ya waya a hankali, kafin ya musu sallama ya bar gidan. "Gaskiya Abdulhakim ya girma yana bukatar iyali amma a ce magidanci irin sa babu mace ai bai dace ba, gaskiya ki tashi a tsaye domin haka bai dace ba" cikin yanayin jimami Hajiya Daulah ta ce mata" ya zanyi tow? Kowa ya juya min baya akan sai dai a bi Shawaran likita" "likita Allah ne? Babu abin da zasu iya idan zaki nima mishi mace wacce zata kula da shi amma abar shi babu mace akwai damuwa." Ai kamar an sosa mata inda yake mata kaikayi ta ce."ya zanyi? Baki daya sun ki amincewa na nima mishi aure, sannan shima har yau yaki maganar auren sai na kawo maganar zai fara kauce kauce. Wallahi na rasa yadda zan yi anya ba hannu aka saka mishi ba?" Kallon juna suka yi baki a bude kafin suka ce. "Tabbas biri yayi kama da mutum."..... African Queen products Sabulun matsi Garin matsi Humra Turaren wuta Maganin Infection Ga number wayata...08130269641 [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan. +234 8130269641 +234 813 731 1900 +234 906 346 7258 +227 84 50 64 76 Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar Top-notch season 2 2023. "Sir Abubakar tafawa balewa* Ya zamu yi? Matukar kika bar shi a haka ba makawa an gama da shi kamar mahaifin sa." Inji Hajiya Nazirah, "Ya zanyi?" Hajiya Daulah ta tambaye ta, "tashi zaki yi tsaye idan ba haka ba, zasu kai ki su baro ki" dag haka ta dauki jakarta tana me mata sallama hade da gargadi me shiga jiki kan shi, domin itama tana son ta samu damar shiga cikin arzikn Hajiya Daulah tun ba yau ba take son shiga itama a dama da ita, shi yasa tana zuwa ta nuna mata hoton Yarta Sophia, domin tarkonta ya kama kurciya, kuma ta samu damar haka sai dai kuma yadda ta tunzura Hajiya Daulah ta kuma nuna mata ai tana tare da ita shine dalilin da yasa Hajiya Daulah ba zata kawo cutar ta zata yi ba. Kuma a tunanin ita sai ta san raunin Hajiya Daulah kuma gashi ta samu. *** Maikulki Duk amintar Malam Aminu da Malam Musa kalla, dakyar da sudin goshi ya bashi dari biyar, itama sai da ya gama jin kamar rayuwar shi yake zarewa zai bashi ya kalli Malam Musa kalla ya washe baki ya mika mishi dari biyar din. "Ai Malam Kalla nasan ai na fita hakkin ka, domin kai ne kayi mana shaida" "tun jiya Juma'a aka baka kudin nan sai yau ka gadaman bani sannan ka dauki dari biyar ka bani anya malam Aminu ka san hakkin abota kuwa? Jeka da shi ma yafe" ya mike yana karkade jikin shi. Tsuru tsuru kafin yayi wuf ya tare Malam Musa kalla. "Shi kenan naji zan kara maka jaka daya a kai kaga jaka uku da rabi kenan" ya fada yana washe baki kamar sauna. "Kasan Allah bani hanya" malam Musa kalla ya fada da ƙarfi, "shi kenan xan kara maka jaka daya da rabi ya tashi jaka biyar kenan." Wani kallon banza Malam Musa kalla ya watsa mishi yana faɗin. "Kaf garin nan waye yake baka shawara na gari? Waye yake maka abin da nake maka maza hada kudinka ka bar nan" "shi kenan ka yi hakuri zan baka jaka ashirin " ya fada yana kallon Malam Musa kalla. A ran ya ce wannan da yasan Bimbi na sayar sai ya kusan kwace kuɗin. "Shi kenan zan amsa amma daga yau babu ni babu kai." Daga haka ya fisge kuɗin, "wai duk akan la'adar ne zai raba tsakanin mu? Indai akan sa ne zan baka jaka hamsin dubu goma sha biyar kenan" wani yalwataccen Murmushi Malam Kalla ya sake yana faɗin. "Ko kai fa, meye amfanin abotar na mu matukar ba zamu ribanci juna ba, madalla ya maganar Bimbi ne?" Gaban sa ne ya fadi ya kalli Malam Musa kalla ya ce mishi." Ya'u zai tafi da ita can birni domin na gaji da ganinta" "abu yayi kyau amma ya maganar niman taimakon da ita" wani irin zabura Malam Aminu yayi yana zare idanu. "A'a bar wannan zancen." "Ai kuwa shi ya dace muyi baka san idan tana birnin shi ne." "Sai an jima idan na fito sallah la'asar zan kawo maka sakon ka." Daga haka ya bar wurin kamar zai tashi sama, rigar shi kuwa iska tana kad'ata kamar an hura mata iska a cikin ta. Koda yazo ya samu ana mata kitso, domin yana fita Shamsiyah tana zuwa gidan. Dake ta iya kitso, ta kama kan tana kitsewa gwanin ban sha'awa. Inna laminde ta zauna tana saka mata lalle, kallon su yayi yaji kamar an cirr mishi duk wani abin da yake kanshi. Su gama wahalar su tana tafiya ta tafi kenan. A gidan Mai gari, kwankwasa kofar dakin shi aka yi. "Yes" "Yallabai Baba yana son ganin ka" "tow" dama zaune yake daga shi sai single da dogon wando. Daukar wani jan shirt din sa da yake gefen shi ya saka, sannan ya rufe laptop din, ya fito yana saka takalmin shi. "Haka rana yayi?" Ya tambayi Nazifi, "eh gashi nan da alamu za ayi zafi sosai " "Allah ya kawo mana sauƙin zafin" "Amin Ya Allah." Nazifi ya fada, zauren suka nufa inda me gari yake zaune yana shan iska. "Barka da Hutawa Baba " "Barka dai Yallabai." Zama yayi yana kallon yadda aka cika gaban Baba me gari da abin tab'awa. "Kayi hakuri Ni nace a kira ka, ka abin tab'awa nan bana son kana zama a dakin nan" murmushi yayi ya zauna yana kallon kayan abincin. "Gashi na koshi Baba " "a'a sai a kai maka d'akin ka" girgiza kai yayi yana faɗin."a'a xan ci ma" ya fada yana dauke kan shi."ya kuka yi da yarinyar nan ne?" Gyara zama yayi sannan ya ce mishi. "Dama ai na gaya maka tun fara aikina, makarantar bashi ya dace da ita ba, akwai makaranta nasu na musamman handicapped iya sune suke rayuwa a wurin, sannan gefe guda domin a kara musu kwarin gwiwa akwai tsirarun dalibai da suke magana da ji, domin su fahimci ba iya su ne kawai ke karatu a wurin ba." "Madalla Allah ya bika." Murmushi yayi yana kallon hannun shi. "Amin Ya Allah." Ya furta, "a sokoton kenan?" "Eh anan cikin sokoton, A.A. RAJI SPECIAL SCHOOL SOKOTO." Mai gari ya jinjina kansa. "Idan za a kaita zan je nima na ga inda take " "babu damuwa Baba, amma ina rokon arzikn don Allah kar ku bari Malam Aminu ya sani tana karatu ne, nafi son ta zame mishi bazata." Ya fada yana kallon Baba mai gari, daga yanayin maganar ya fahimci abin da yake nufi don haka ya jinjina kai yana faɗin. "In sha Allah, zamu yi kokarin haka." Sun jima suna tattaunawa akan haka. Kafin aka kira sallah azhar suka tafi masallaci. A masallacin ma Malam Aminu wasan boya suke da Abu turab, domin baki daya sai yaji tsoron kar Abu turab ya kunyata shi a cikin jama'a. Shima Abu turab ya fahimci haka, sai yaki yarda su hadu da Malam Aminu din tunda yana gudun shi ne. Shi kansa Malam girmama abin yake amma bai wani damu ainun ba, domin gani yake kamar ai ya rabu da karfa ne domin idan ba haka na, zai ta damun shi. A can kuwa Inna Laminde har da lalle aka yiwa Auta. Kome nata gwanin ban sha'awa. An daka mata yaji da soyayyar jar miya aka zuba a gwangwani, ga yajin karago da yajin daddawa, dai jar yaji. Sai garin kwaki da gyada da dakakken kanzo. Da maggi leda guda. Inna Laminde da sakalta autar ta, har da yanka mata zabi guda biyu da wani matashin agwagwa, aka hada mata a kan jar miyarta, manja a karamin gora da mangyada. sai gishiri da sabulun wanki man shafawa, man kitso da man kad'anya. Kayan dai gasu nan. aka saka a cikin Ghana most go, daidai kunnen da take ji Inna Laminde ta tsaya tare da rike mata shi. Tunda ta ga haka ta fahimci fada ne, rau-rau tai da idanunta tana kallon kasa.. "ina gaya miki babu ruwan ki da kowa karatu ya kai ki ba shiga hurumin da ba naki ba, sannan haramun ne sata da wani aikin Asha idan baki da abu za a baki lambar Yayanku ki saka a kira shi kin ji" gyada kai tayi hawaye na zuba mata, ta tsani fada a rayuwarta, shi yasa take kiyayye abin da za a mata fada, musamman ita da Baffan su ya tsane ta. Haka suka yi suna faman shirya kayanta. Har da busashen ramma, da yamma ta mata wanka domin Ibrahim zaizo da wuri tafiya da ita Sokoto har da Inna. Bayan isha Malam da yake rike da radion kamfanin Kachbo, ya kalli Laminde ya ce. "Kowa yaci zomo, ya ci gudu ban ga amfanin hana kai sararawa ba wallahi" juyawa tayi duk da babu wadataccen haske sai na fitilar kwai ta juya ta zabga mishi harara. "Malam kenan, ai kowa yaga balbela da farinta ya ganta, kana tunanin zan iya baza hakarkarina a shimfida ban kula da amanar da Allah ya bani ba ne? Ko ka yarda ko kar ka yarda ba a sauyawa tuwo suna." "Wa ni? Tow wallahi na kusan yarda mangoro na huta da kuda, hmm baki san dawar garin ba ne." Ya fada yana kara karar radion. Bata kula shi ba, ta ci gaba da aikinta, da ta gama ta wuce dakin ta. Wa shi gari tana sallah asuba ta tashi da kimtsa ɗakinta, suka karya wurin karfe goma sai ga Ibrahim da mota.a gurguje suka fitar da kayan suka wuce, domin rana ta fara yi. Koda suka fito sai da suka tsaya a gidan mai gari, suka wuce. Wurin karfe biyu zuka isa Sokoto. Gidan Zakaria suka nufa, matar shi yar me kirki ta karɓe su, ta fara hidima da su. Dake Sa'ade tana zuwa Inna ce dai bata cika zuwa ba. Abinci suka sannan suka huta. Matar Zakaria me suna Ummi ta shigo suka gaisa. Inna laminde ta ce mata. "Ummi ga dawainiya nan na kawo miki, kin san halin Baban naku. Don Allah ga Autana shi yasa nazo da kaina na roki Alfarmar ta zauna dake, ba don tana kanwar shi ba, a'a ki dauketa a matsayin kanwar ki, kafin Allah ya kawo miki naki. Idan Allah yaso zan na zuwa duba ku. Idan na samu lokaci" "Allah sarki Inna in sha Allah babu abin da zai faru. Na gode sosai domin tuntuni nake son a bani Sa'ade kika yau gata Allah ya kawo min ita, Alhamdulillahi." Auren su kusan shakara bakwai amma har yau Allah bai azurta su da haihuwa ba. Haka suka wuni a gidan itama Ummi ta kara mata da su kayan zaki a biscuit da chocolate, washi gari ya kama Monday. Bayan sun karya Inna ta ce mishi. "Ina son raka ta, amma ina jin kar ta min kuka ne" "Kai innah Sa'ade shekaran ta tara saura watani ta cika goma, idan an kaita aji biyar zasu bata, domin ta kara kwarewa a karatun su, muje ba zata yi kome ba, amma zan fara zuwa aiki idan mai gari ya iso zan zo na dauke ku" "tow Allah ya muku albarka baki dayan ku, a dawo lafiya" ta fada. "Amin Ya Allah" ya ce. yana fita da sauri. Sa'ade tana wurin Ummi suna wanke wanke, kallon su Inna tayi daga dakin da suka sauka, a ranta ta ce. 'Alhamdulillahi ko mutuwa nayi Sa'adatu ba zata yi maraici ba.' kwanciya tayi barci ya ɗan yi gaba da ita. Abuturab da Mai gari wurin karfe daya suka iso Sokoto, in da suna tsaya a kofar makarantar. A.A. RAJI SPECIAL SCHOOL SOKOTO, yana parking ya kira Zakaria. "Assalamu alaikum, mun iso ga mu a bakin makarantar." "In sha Allah mu ma, gamu nan zuwa." Zakaria ya fada. Sun kai minti Talatin a wurin kafin Zakaria da su Sa'ade da Yusuf da Inna, tare da Ummi suka iso makarantar. Buɗe musu kofar shiga makarantar aka yi musamman motar Abuturab da yake da plat Number na gidan Sarkin Musulmai. Gashi lokacin an tashi kenan daga makarantar dalibai ta ko ina, sai bin motar ake da kallo. Har suka isa bakin office din Shugaban makarantar, daga yadda Abuturab yake tafiya zaka fahimci yana da masaniya da wurin. "Prince kun iso ne?" Yarima Sadeeq ya iso da dan sassarfa yana mika mishi hannu, buge hannun yayi yana hararan sa. "baka ga baki bane" mikawa Baba mai gari hannu yayi suka gaida. "Mai garin Maikulki na karamar hukumar Binji." "Ni kuma Abubakar Shehu Abubakar. " "Yallabai Barka " Mai gari ya fada cikin girmamawa. "Zakaria Aminu Fulani " "Yarima Sadeeq." Shima Sadeeq ya fada, "amma kamar kana program a Radio station ko?" "Eh" "Yusuf Aminu Fulani, ga Innar mu, wancar kuma matar Brother ce, Mrs Zakaria Fulani, ga Sa'adatu Aminu Fulani." "Great family nice to meet you." Sannan ya juya ga Abuturab da ya koma gefe yana waya, ba zaka.iya tantance abin da yake fada ba. Amma yadda Sa'ade ta sake baki tana kallon shi zai baka dariya. Domin abin da yake ko ita da take auta ba tayi. African Queen products Sabulun matsi Garin matsi Humra Turaren wuta Maganin Infection Ga number wayata...08130269641 [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan. +234 8130269641 +234 813 731 1900 +234 906 346 7258 +227 84 50 64 76 Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar Top-notch season 2 2023. Kamar a ce ya d'ago kan sa suka yi ido hudu da ita, da sauri ta sunkuyar da kanta, duk da ba wani lokaci suka dauka ba, sai dai ta fahimci shi babu ruwan shi, kuma be damu da rashin maganar ta ba, asalima shi ne mutum na farko da ya gwada mata zata iya karban duk abin da ya zo mata, d'age mata gira yayi ta kuma sunkuyar da kanta. Kashe wayar yayi ya ce. "Muje ko" "tow" principal da mataimakin sa ne suka fito daga office din su, suka tare su. Cikin girmamawa tare da mutuntawa. "Sannun ku da zuwa" "yawwa" suka bashi amsa ban da Abuturab da yayi shiru yana sauraron su. Shi da mai gari suka zauna, Inna Laminde da su Zakaria da Sadeeq suna tsaye. "Barkan ku da zuwa" principal ya kuma fada yana kallon Sa'ade. "Ita ce dalibar mu?" "Eh Malam ga Sa'adatu nan mun kawo maka ita. " Inji me gari, "toh madalla, kallon Abuturab yayi sannan ya ce mishi. "Yallabai me kake bukata a yi ?" "Special class ina son ta samu ilimi me kyau" "in sha Allah " sannan suka shiga tattaunawa daga akan matsalarta. "Vice kira min Malam Ayuba." "Shi kenan " da sauri ya fita domin an riga da an tashi, masinjan su ya gani ya gaya mishi ya kira mishi Malam Ayuba, can kuwa sai gasu tare. Office din principal suka nufa, suna shiga principal ya d'ago hannu zai mishi magana Abuturab ya rigashi, inda ya mika tafin hannun shi, ya saka dayan alamar "ina wuni?" Cikin farin ciki Malam Ayuba ya amsa mishi yana faɗin. "Lafiya lau." Nan hira ya barke tsakanin su, murmushi principal yayi yana faɗin."Shi kenan sai ka mishi bayani shine for master jss 1, ajin shi zata zauna" sake kallon shi yayi ya janyo Sa'ade ya nuna mishi ita. "Yar uwata ce kuma naji ance kai ne malamin su?" "Eh yallabai ni ne malamin su." Ya fada, "tow gata nan na kawo maka ita, don Allah ka kula da ita mun gama kome tun wancan lokacin" "shi kenan ba kome zan yi yadda kace ai nima yar uwata ce tunda laluran mu daya bamu kyamar dangi." "Na gode sosai da kulawar da ka bani." "Nima na gode, zamu iya zama abokai?" Murmushi Abuturab yayi ya mika mishi hannu, daga nan ya ja su, zuwa staff office aka kawo register na yan Form one, aka saka sunanta. Shi da kansa ya nimo wasu senior kurame, ya damka musu Sa'ade a hannunsu, anan fa Sa'ade tace bata san zancen ba, domin dai ba zata bisu ba Inna Laminde zata bi. Dakyar aka lallabata domin basu so ta saka a ranta cewa ba a sonta, mota Abuturab ya bude ya dauko wani karamin kwali ya mikawa daya senior din ya durkusa yana kallon Sa'ade ya saka hannu a wuyar shi alamar na rantse. "Zan kawo miki innar ki da su Yayaun ki." Ƙaramin yatsanta ta mika mishi alamar " Alkawari zaka kulla" "na kulla " ya mika mata yatsar shi, suka kulla alkawarin zai dawo. Daga haka suka bar makarantar, lokacin da aka kai Ummu Mansurah special school haka suka yi, domin a lokacin gani suke kamar ba a kawo musu visiting ba. Tana waiwaye tana kallon su har suka b'ace. "Malam Abuturab mun gode Allah ya saka da alkhairi mun gode sosai. Allah ya raba ka da sharrin abokan halitta." "Amin Ya Allah " kallon shi Inna Laminde tayi ta ce mishi. "Ubangiji ya tsare ka daga duk abin ki, Ubangiji ya sakawa da iyayen ka da alkhairi, Allah ya daura ka saman makiyan ka, mun gode mun gode da ka mai da Sa'ade mutum, domin har na fara hango iyakarta daga makarantar Maikulki shi kenan " murmushi yayi sannan ya ce. "Muje a mai daka gida Baba Mai gari zan leka cikin gida ne" "mun gode sosai." "Maman Sa'ade mu tafi tare mana " "Tow ranka ya dade, nima ina son bin ku kuwa" inji Yusuf domin ya kwana biyu bai shiga Maikulki ba. Haka suka nufi inda motar da zai kai su gida yake ajiye anan suka kara godiya sosai, sannan motar kiran hilux ya ja su. ____Sa'ade bata tab'a tsammanin akwai irin wannan yanayin da rayuwar ba, sai da aka shigo mata da katifarta da zanin gado, seniors din nan suka shimfida mata, ta zauna tana cire takalmi, sai kallon kwana da kwana take, lumshe large eyes dinta tayi, kallon wasu yara biyu yan mata a gefen gadonta. Daya a cikin su tana cikin kwadon garin kwaki, mika mata tayi ta girgiza kai. Kallon Seniors din na saman gadon Sa'aden tayi, ta tab'a tana tambayar ta, "ya sunanta?" Kallon Id din Sa'aden tayi ta mika musu. Mikawa na saman tayi tana mata alama da hannu. "Dama muna niman wata kawa saura ta hudu ko?" Gyada kai tayi, suna zaune senior suka shirya mata kayanta, da zasu tafi dayan ta riko hannunta ta haɗa da na yan matan tace musu. "ga kawa na kawo muku, ban da fada ban da rigima idan kun samu matsala da wasu ku zo ku gaya mana. " Ta musu alama. Gyada kai suka yi, duk da bata cika gane maganar su ba, tunda ba wai ta taso da masu ba ne, me mata kenan Malam Bature. A kwai wani dabi'a da kurame ke da shi, kaf duniya babu wanda ya kai su, kaunar nasu. Sannan suna matukar girmama me yanayin su, wato me laluran su. Haka yasa dakin baki daya da suka fahimci Sa'ade itama Kurma ce, zo kaji yadda aka sakata a gaba da nuna kauna da kulawa. Basu daina Yaren su,sai da metro din su Baba Kande ta shigo, suna ido biyu da ita kowa ya kama gaban shi. Kallon su tayi tare da musu dakuwa, da sauri suka haye gado, domin an jima zasu sallah da amsar abinci. Dole su kwanta su huta. Kafin lokacin yayi "Well-done my Man ka kyauta." "Ina son zuwa kwara amma dole sai an samu hutu tunda sun kusan fara jarabawa nan da sati tara" ya fada in low voice, kasancewar garin akwai hadari ga wani iska me dadi da sanyin, kana ga kamshin damina, kallon Sadeeq yayi yana faɗin. " Weather yau yayi dad'i " "Ba laifi muje" haka suka shiga motar Abuturab din, suka shiga tafiya yana jin wani irin dad'i da nutsuwa a ran sa. Koda suka isa kan wuri sun samu tarba me kyau, sannan ya ci abinci ya wuce dakin su ya kwanta, kiran sallah azhar yasa shi mikewa yayi alola ya nufi masallaci basu dawo ba sai la'asar, yana dawowa ya fara aikin shi. Har magriba koda suka tafi masallaci basu dawo ba sai isha abincin kawai ya ci, ya kwanta bai kuma bin ta kan Yarima Sadeeq ba, sai barci. Wuraren asuba ya farka sakamakon wani irin mafarki wai yayi da Mansurah cikin jini. Da wani irin mutuwar jiki ya tashi dakyar ya shiga ban daki, yayi wanka da alola ya dauko wani jallabiya fari ya saka, sannan ya fesa turare, ya nufi masallacin yana me saka counter a hannun shi, ana idar da sallah ya dawo cikin gidan ya shirya ya nufi wurin motsa jiki. Duk da ya gaji amma ya rasa me yasa ake boye mishi inda Ummu Mansurah take, haka ya dawo gida, idanun shi ya sauka akan matasan kwanaki duk da dayan zai iya girme mishi, da alamu wa da kani ne. Tab'e baki yayi ya wuce abin shi, akan lokaci ya wuce cikin gidan ya shirya ko karyawan bai yi ba, ya nufi inda motar shi yake ya koma inda yake bautar kasar shi.. Kwana ɗaya babu Sa'ade, Inna Laminde sai da taji wani irin kewar Yarta, kwana tayi tana jin wani irin d'aci lokacin da Mai gari take bata labarin ai sayar da Laminde Malam Aminu yayi tayi kuka ainun domin bata kawo kiyayyar ta kai har haka ba. Ta zata kawai yana kinta ne domin bata ji bata magana, ashe kin jininta yake tunda tazo a kaddran. Bata tab'a sanin cewa zai iya sayar da yar shi kamar Saniya ba, asalima Saniya tafi ta daraja sai yau da take jin labarin abin da ya aikata ashe dabba tafi dan mutum daraja? Hawaye ta share domin an kai limit din da zata iya zama da malam Aminu ba, halin shi ya gundire ta, zata bar mishi rayuwar shi yaci kansa da wadanda yake so. Haka ta kwana cikin bakin ciki da b'acin rai. Washi gari kuwa. Ta tashi abin ta tana kallon sa yadda yake ta kiciniya da saniyar sa. "Malam baka ji kunya sayar da dan mutum madadin saniya ba?" A firgice ya juya yana kallon ta, a ina taji wannan mummunan labarin? Waye ya tona mishi asirin shi a gaban iyalin shi. "Allah yana ganinka! Kuma yana ji yana gani sai ya muku hisabi da Yarka, duk cikin yaran nan ita ce daya ta tashi bata san soyayyar Uba ba, domin ƙaddara ta same ta, malam ka gaya min yaushe zaka mutu? Ka san ranar mutuwar ka ne? Yarinya na babu ruwan ta ka sayar min da ita meye laifinta? Nace meye laifinta. Allah sarki yarinya karama da bata ji ba bata gani ba. Ta fuskanci jarabawar rayuwa ka je mun barka da sallah." Ta fada cikin matsanancin kuka. Domin ya kaita bango, "na gaji da halin ka na gaji da fitinarka zan tafi na bar maka gidan ka sai kaci kanka da kanka." Ta koma daki tana kuka domin iskancin Malam ya shure tuninta. *^^^ A hankali take shirya tana kallon yan matan nan. Ganin yadda suke shiri. Kallon abinciin da suka amso jiya suka yi na ta bata ci ba. Domin munin tuwon yasa bata iya ci ba, domin wannan ba irin girkin Innar su ba ce ko Inna Larai girkinta duniya ce. Tuwon datsa ne, sannan miyar kana ci kana jin dunkulen kuka. Bude kwalin gaban lock ɗinta suka yi, tana kallon su bata ce kome ba. A hankali suka ciro golden more da madaran gwangwani, Sugar kwali, suka mike tare da dibo ruwa suka hada mata. Sannan suka mai da kwalin suka rufe, wacce ta haɗa mata ta lock din ta shiga cusa kayan cikin kwalin tass suka fitar da wanda basu da wasu anfani a cikin lock din. Suka shirya tsaf. Sannan suna rufe mata kayan tare da bata key. Murmushi suka yi, daya babban ta mika mata ID dinta. Rahilah Adam Gwarzo, ta nuna kanta tare da juya hannunta. Ma'ana sunanta. Ita kuma daya ta nuna mata Husnah Jafar Kurmi, sai itama Sa'adatu Aminu Fulani, haka suka jira ta ta gama sha ta ma koshi, kallon su tayi domin ta iya magana da idanu tare da gira, har Gara giran Abuturab ne ya koya mata, a yar zaman su. Idanu kuwa dama daga ita sai Innarta suke maganar da idanu. Kamar da wasa sai ta ga sun amsa mata suma. Mika musu kofin tayi, tare da mata alamar a "kusha" girgiza kai suka yi Rahilah Adam Gwarzo ta nuna mata. "Yanzu na sha kwaki da madara sai dai ko Husnah Jafar Kurmi" girgiza kai tayi tana mata alamar. "Na koshi muje nasan yau koko ne ki dauki suga gyada." Haka ta dauka suka dauki kofin suka rufe mata tare da sakawa a locker suka bar hostle. Dinning suka nufa, sai da suka wanke kwanon su sannan suka shiga sai da suka bi layi, sannan aka zuba musu kunu da kosai ne. Suka samu wuri suka zauna suna sha. Duk da a takure suke sai take jin dadin haduwar ta da Rahila da Husnah. Can gefe makafi ne suna amsar nasu, ta bangaren kurame babu hayaniya sun gama karban abincin su, amma bangaren makafi Wayyo Allah. Hayaniya har turereniya. Karshe sai da masu saka abincin suka tsawata musu. Haka suka kammala cikin abincin suke bar hall din, suka nufi dakin su, tare da ɗaukar jakunnan su. A hanya gudu suke har suka isa Aji, suka isa bakin kofar suka fashe da dariya, daga nesa Sadeeq yake hangonta. "Yarinyar ta sake ta samu wasu yara biyu kuma ina ga yanayin su daya." Ya fada s wayar da yake da Abuturab. "Haka zai taimaka mata wurin karatu, matukar ka samu wanda halin ku yazo daya zaka yi karatu sosai." African Queen products Sabulun matsi Garin matsi Humra Turaren wuta Maganin Infection Ga number wayata...08130269641 [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: "Ya batun sayanta da kayi?" Sadeeq ya tambaye shi, shiru yayi domin ya manta batun ma wallahi, kawai ya fadawa Sadeeq din ne domin ya taya shi jajjantawa. "Shhhhhh, ka manta da batun abin da ya faru na sayanta da nayi, sauran zan duba al'amarin, sannan don Allah ya zama sirri a tsakanin mu " dariya Sadeeq yayi sannan ya ce mishi. "Ko kana kiwontawa kanka ne?" "Meye? Me kace?":"A'a bance kome ba, zan taya ka saka idanu akan ta, kuma zan hana wani saurayi ya ce yana sonta nasan nan da shekara biyar ta zama Yan mata" "Mtseeeeeew baka san ina da yarinyar da aka mana baiko ba ne? Don haka ka bar wahalar da kanka" "Baiko ba aure bane za a iya maku baiko idan Allah bai nufa akwai auren ba sai ta mutu ka fahimta " "Allah ya shirya ka" haka suka yi ta wayar su har Sadeeq ya kashe wayar. A can class kuwa gaban class Rahilah ta jata suka zauna a sit din gaba suka zauna suna dariya. Minti goma da shigowar su ajin Malam Ayuba ya shigo suka mike tare da Gaishe shi, sannan suka koma mazaunin su, fitar da kundin ajiyar sunayen su yayi, ya fara kiran sunan su. *** Abdulhakim. A yan kwanakin da Mahaifiyar sa, attajira Hajiya Daulah wani irin rikici take ji domin ta kara mishi masu kula da lafiyar shi, wato escort. Duk inda zai shiga suna biye da shi kamar bindi. Wani abin damuwar shi ne yadda ta saka shi a gaba da maganar aure, tun yana kaucewa har ya koma zata saka shi a gaban Kannen shi tayi ta fada da masifa. Idan ka gan shi yana da matukar sanyi da hakuri, duk fadar da take bai ce mata cika kanki ba har ta gama. "Duk abin da nake maka ina yi ne domin ina kaunar ka babu uwar da zata so danta ya kai kusan shekaru arba'in babu mace." "Hajiya amma ai kin san matsalar sa. Zai ajiye mace ne babu biyan bukata? A ajiye ma zancen ya ajiye mace zuciyar shi bata bukatar wahala. Idan har lokacin auren yayi zai yi ba, shi aure lokaci ne don Allah ki daina damun sa da zancen aure domin zai yi babu wanda ya isa ketare kaddaran sa." Dr Sharif ya fada yana shigowa falon wani irin ajiyar zuciya Abdul ya sauke a sirrance yana kara damke hannun shi da juna, domin ya tsira tunda mahaifin su ya zo akan lokaci, a fusace ta juya tana kallon shi. "Kace nayi hakuri na zuba mishi idanu? Wani irin ciwo ne haka da za a ce mutum ba zai yi aure ba " "zuciyar shi ba zata iya daukar nauyin bukatar shi na D'a namiji ba, idan kuma kina ganin auren shi ne mafita sai ki yi mishi ai tunda baki da lissafi." Ya fada yana zama a daya daga cikin kujerun falon. "Kamar ya bani da lissafi? Bayan duk abin da nake a lissafe yake " "Taufiq bani ruwa na sha, domin ita bata san yadda ake tarban miji ba" ya faɗa yana kallon ta. "Alhaji kar kace zaka biyo ni gida na kaci min mutunci." Cire hular kansa yayi ya amshi ruwan da Taufiq yake bashi. "Ko daya sai dai akan Abdul ne zamu iya samun matsala sosai. Wajibi ne ya miki biyayya na wacce ta haife shi, kare rayuwar shi kamar dole ne a kaina, domin ba zai yiwu ki kashe min shi ba." Zama tayi tana faɗin."Amma ai ba wani abu ba ne tunda auren nan kare mutuncin sa zai yi ba kuma." "Kin ga tsakaninki da Allah kin tab'a jin ko ganin yana kula yan mata?" Girgiza kai tayi, shi kuma yayi murmushi. "Ba da lafiya, idan har ya ce zai kula mace taya zai kula da ita bayan shi kansa bukatar kulawar mace yake nima? Ba wai ina bayan sa bane a'a kawai ina so ki gane idan macen da yake bukata ne zai zauna da ita, musamman idan shi yace yana sonta. Su yaran da kike hangowa idanun su a bude take idan kika haɗa su da Abdul wallahi kece zaki dawo kina zaman jinya, zuciyar shi ba zata dauka ba, ki kira likita ya miki bayanin condition din sa." Gyada kai tayi tana faɗin."Hmm! Wato yadda aka tsara ka haka zaka zo ka saka min magana a bakina Yarona daya tal da yake kula alamarina shi zaka ce na" "Hajiya ba haka bane amma gaki ga shi duk abin da kika yi me kyau ne " ya mike tare da wucewa upstairs. Tashi tayi ta bishi itama don haka ba karamin kai ruwa rana suka y ba, domin gani take kamar karya ne taya za ace kar yayi aure fada me sunan fada suka yi wai don ma shi yaki kula ta. Domin irin mutanen nan ne da basu son abin kunya a cikin iyalin su. Da taga yaƙi kulata kawai ta shiga fashe fashe kamar mahaukaciya, tana ihu da magana marasa dadi da kyau, wucewa daki Abdul yayi ya zauna tare da rike kansa. Maganar likita yana dawo mishi mishi tiryan-tiryan. "Idan nace zaka yi aure a madadin a samu zaman lafiya sai a samu matsala domin babu macen da zata zauna da kai babu sauke hakkin aure. Ita kanta zuciyar da zata yi wannan aikin babu lafiya da karfin da zata yi,kaso cassa'in na jin dadin rayuwa aure yana tare da sarrafawar zuciya ce, idan har baka samu macen da ta fahimce ka ba, zaka sha wahala sosai. Domin karfen da aka saka maia ba zata yi aiki yadda ya dace ba. Ka gane abu daya bugun zuciyar ka zata iya wuce iyaka matukar ka nace sai kayi tarayya da ya mace. Shi yasa muke kokarin ganin ka iya sarrafa na'uran cikin zuciyar koda kuwa sha'awa ce ta mafarki ta sarrafa ta. Amma abin ya ci tura" girgiza kai yayi yana faɗin. "Dr bana iya kallon mace ne, anya zan iya samun damar aure kuwa? Dr!". Murmushi likitan yayi yana faɗin. "Zaka iya aure har ka haihu, sai dai ba abu me sauki ba ne yin auren da haihuwar kafin ka samu macen da zata iya rayuwa da kai shi ne matsalar, amma ba wai ba zaka samu ba ne, zaka samu fa ka cigaba da shan magani xaka samu macen da zata zauna da kai." Bude fuskar shi da ya rufe da tafin hannun sa yayi yana jin wani irin damuwa da kunci a ran sa. *** Maikulki. Duk da cewa ya tsani ganinta amma yau kwana biyu kenan bai sakata a cikin idanun shi ba, ko ba kome itama Yarsa ce. Duk da yadda yake azabtar da ita bai tab'a kawowa zai ji a cikin kwana biyu rak yana bukatar ganin Yar da ya ke da yakinin bata da wani amfani a cikin gidan sa facce zama cikin gida domin kar ta janyo mishi na kasu a jikimar sam, zuba tagumi yayi yana kallon yar tinkiyarta. Ko ba kome yayi kewar mace ta. Tashi yayi zubur ya shure kofin silver da aka saka mishi koko me suna mai gida jaki. Ya nufi wane fuuuu. Kallon shi Inna Larai tayi tana faɗin."Allah ya kyauta. "Kai dai Malam baka da hali" ta fada tana dauke kofin kunun. Tafiya yake kamar zai tashi sama, duk inda ya wuce sai an bishi da idanu, kofar gidan Mai gari ya nufa, daidai Abuturab ya fito daga cikin gidan kenan. "Malam Bature sallama" ya fada yana ja da baya, domin yadda suka yi ido biyu da Abuturab ya ɗan bashi tsoro. Kuma dake yasan yayi rashin gaskiya take Abuturab ya cika mishi Idanu "Baba kai ne?" "Eh Ni ne" Malam Aminu ya fada yana ja da baya kaɗan. "Toh ja da bayan na meye? Baba sake kayi magana mana" "Dama nazo ne akan na tambaye ka ina kasa suka kai Bimbi?" Juya kai yayi sannan ya kalle shi na wani lokaci kafin ya ce mishi." Kana bukatar ta ne yanzu?" Abuturab yayi magana cikin nutsuwa da kamewa kamar ba sangartaccen nan ba. Hàdiye yawu yayi makwat yana kallon shi. "Dama.... Dama..." Ya kama in-ina, "matso na gaya maka yadda nayi da ita " matsowa Malam Aminu yayi yana zare idanu. "Ka sake wani ya san sirrin mu yanke maka kai zan yi, domin ba zan iya jure zaman gidan yari ba, tunda kai ne ka sayar min da ita ba saka ka nayi dole ba, don haka ka sha min lafiya." "Wa'iyazubillahi." malam Aminu ya fada a tsorace, "kasan hukuncin wanda ya sayar da mutum kuwa? Tow wallahi karka bata min sana'a kai ma ka kula domin zan saka a sace min kai don haka ka saka zare da allura ka dinke bakin ka" rufe bakin sa yayi jikin sa yana rawa. "Anya zan yarda da kai kuwa?" "Na rantse da Allah ba zan maka kome ba" "anya maganar ta kai zuci kuwa?" " Gasken gaske babu abin da zan maka" shiru Abuturab yayi kamar me nazari kafin ya ce. "Tow zan yarda da kai amma bisa sharadi kullum zan zo gidanka da maraici domin kar ina zaune ka kawo min jami'an tsaro ban sani ba." Tsuru-tsuru malam yayi kamar zai fasa ihu ya ce. "Ina cewa ba gayawa iyalina zaka yi ba abin da ya faru? Sannan a ina Uwar Sa'a taji labarin na sayar da ita?" Wani kintaccen kallo Abuturab ya mishi tare da cewa. "ka tab'a gani na a gidanka?" "A'a billahi lazi ban tab'a ganin ko inuwar ka ba " "toh tunda baka tab'a gani na ba, shi ne zaka min sharri Baba bani kudina na fasa sayan ta, tunda ban maka abin Arziki ba. Bani zan saka su dawo maka da kurman Yarka, kasan kuwa har mijin aure zata rasa idan al'umma suka ji labarin sayar ita kayi, ita kanta tsanar ka zata yi don Allah bani kudina na fasa sayar maka, domin idan yan sanda suka zo kama ka, kar su kama ni ai ban san haka kake ba." Wani irin rawa jikin Malam Aminu ya dauka kamar zai sake fitsari a wando, domin har ga Allah bai kaunar ya kara komawa wurin yan sanda ba, ya san mugun dukan da suka mishi. "Don Allah ka rufa min asiri." "Ai Baba baka san wani ba, hukuncin mutumin da ya sayar da mutum yanke mishi hukuncin kisa ake, don haka maza ka dawo min da kudina domin ba yarda zan yi ba" "Ayya d'an nan kayi hakuri na tuba k yafe min" shiru yayi yana kallon Malam Aminu kafin ya kalli agogon hannun shi, ya ce. "zan tafi makaranta domin ja janyo min na makara. Dole na shiga mota kenan, muna ma magana ne ko? Tow wallahi naji labarin wani abu ya faru tabbas sannan kasan ana tuhumar ka da laifin safara kwanaki ko? . Zan sayar da kai ina ganin kai kan kafarka zasu saya domin." Bai rufe baki ba ya hango malam Aminu can ya arta a guje, sai lokacin ya sake murmushi domin ya fahimci tunda malam Aminu yaci duka Allah ya daura mishi tsoron yan sanda, balle kuma al'amarin ya kuma lalacewa da zancen sayar da yar shi. Nufar makaranta yayi, sai murmushi yake lokaci zuwa lokaci har aka tashi. Al'amarin Malam Aminu kuwa, tsoro da fargaba suka mishi diran mikiya, take wani mugun zazzaɓin tsoro ya kama shi, kafin kace kwabo cikin ya murde sai gudawa, dakyar ya ke kai kan sa ban daki domin ya gama firgita sosai. Wurin karfe daya sai ga Abuturab, ya kuwa buga sallama. Zuru-zuru malam Aminu yayi jikin shi yana kerma ya juya yana kallon kofar dakin zauren shigowa gidan sa. "Barka da Baba? Babu kowa ne a cikin gidan?" Ya fada yana murmusa mishi. "Kululu" ya rintsa idanun shi." Kafin ya mike dakyar ya nufi kofar ban dakin yana shashekar kuka. Domin har ga Allah abin ya burge shi yana son Malam Aminu ya girbi abin da yayi ne. Kuma da alamu kwalliya zata biya kudin sabulu...... ASHRAF, SANIN GAIBU,TSINTUWA is not free, Pay N400 ONE, TWO N800, THREE 1K to 0008219237, Jaiz bank Azizat Hamza Kar ku manta zaku iya biya ta nan, katin mtn sai ku turo mana ban da VTU evidence din ku ta waɗannan layikan. +234 8130269641 +234 813 731 1900 +234 906 346 7258 +227 84 50 64 76 Mutanen mu na kasar Nijar zaku iya biyan kudin ku ta wurin Nana A'ishah nijar Top-notch season 2 2023. African Queen products Sabulun matsi Garin matsi Humra Turaren wuta Maganin Infection Ga number wayata...08130269641 [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: "Wa'alaikumunsalam Barka da zuwa, lale lale." Inna Laminde ta shimfida mishi taburma a tsakar gidan tana faɗin. "Ashe zaka shigo?" "Eh Inna ga ni, ya mutanen gidan mai gari¿" "Suna lafiya." Wucewa tayi ta kawo mishi ruwa daga randan kasa, yayi sanyi sosai ya ce. "Sannu Inna har da wahala" "ba wahala ba ne yiwa kai ne" ya fada idanun shi yana kan kofar ban daki. Ko ba kome ya samu wani weakpoint ko ya ce jackpot na Malam Aminu, a ban dakin kuwa ji yayi ina ma da tare da uwar hanjin shi ran shi zai fita ya huta da kallon da Yaron an yake mishi, asalima kin fitowa yayi, ya zauna abin shi yana jin hiran tare da jiran tsammanin yaushe Abuturab zai tafi ya fito. "Malam lafiya kuwa? Har yanzu bai fito ba." A ran Abuturab ya ce. 'Ina zai fito tunda yasan abin da ya shirya' a kan fuskar shi kuwa murmushi yayi yana faɗin." Ba mamaki uzurinsa bai kare ba ne" Sai da Malam ya shafe minti arba'in a cikin ban dakin kafin ya fito yana rike cikin sa. "Sannu malam" "yawwa Larai" ya fada cikin wata irin murya kamar me shirin fashewa da kuka domin dai ya rasa yadda zai da abu turab. Haka suka gaisa sama sama. Idan ya kalli fuskar Abuturab wani irin kwarjinin tsiya yake masa don dole ya kwanta kamar mara lafiyar gaske. Haka Abuturab ya karaci hiran shi yayiwa su Inna sallama. Bayan ya musu alkhairi dakyar ta amsa, domin ba zata iya wannan abin kunyar ba. *** Kwara Zaune suke surukanta musamman Hajiya Mariya da take kamar zata shige cikin Sultanate. "Sultanate maganar Fadwa akan Yaron nan nake son ki tuntubi Sultan akan su, manemanta sun matsa lamba" shiru tayi na wani lokaci kafin ta ce mata."amma kin san dai ba zaki daurawa dana dawainiyar auren kanwarki ba?" Ta fada in serious tone. D'ago idanun Hajiya Mariya tayi kafin ta kalli yadda kishiyoyinta biyu suke murmushi suna rufe bakin su. "Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana. "In sha Allah zan dauke kome?" D'ago kai Sultanate tayi tana kallon Hajiya Mariya. "Na ga baki aikin fari balle baki a ina kike samun ki? Ko kin fara dauke-dauke kika fara a turakar Abdurrhman?" Maganar ta daki Hajiya Mariya. Shanyewa tayi cikin basarwa ta ce . "Subhanalillahi sai kace ban gaji arzikn ba Sultanate? Ai kome lalacewar gawar giwa tafin kiyashi ya jata." Kur Sultanate ta mata domin bata ka kawo data mata irin wannan reply din ba, ta zata shiru zata yi tunda Gulma ce ke kawo su kullum, sai yau taji saba'nin haka. Ita Sultanate duk abin da za a ce danta yayi yayi ko da kuwa hakkin da ya dace ya sauke ne sai ranta ya b'aci balle kuma abin da ya shafi iyalin shi ne kuwa. Shi yasa ta tsani Badi'atul Noor domin babu dalilin da zai saka ta tambaye ta abin da take bukata sai dai shi tsakanin d'a da uwa ya gaya mata gaskiya abun da yayi, haka yasa take mugun tsanar Badiatul Noor da yaran ta, domin ta ce kome ya samu a jikin Badiatul Noor yake kare baya tuna bayan shi. Jim tayi tana kallon Hajiya Mariyah da ta gama cika ta batse."tow Allah ya kyau lokacin, amma ke kuwa guda nawa Fadwah take da har zaku fara zancen aure " gyara zaman Hajiya Mariyah tayi tana faɗin. "Gaskiya kan bata wani girma ba, amma Sultanate shin me yasa kike jin babu dad'i ga mutuwar Mansurah? Naga tsarar Fadwah ne don haka ina ga it is best time a aurar da ita tunda gana da wanda take, ban shirya ganin hawayena yana zuba ba, Allah ya basu zaman lafiya. Na gode." Ta fada tana barin falon. A karon farko da taji masifar tsanar Sultanate domin ta lura a duniya son kan Sultanate yayi yawa. "Mariyah bamu gama magana ba, zaki tafi? Waye ya baki wannan kwarin gwiwa haka ne?" Shanye bacin ranta tayi tana kallon Sultanate sannan ta ce mata. "afwa ina da abu me muhimmanci ne shi yasa, Allah ya huci zuciyar ki" daga haka ta fita.. Abin ya bawa Sultanate mamaki, wato idan ta lura Badi'atul Noor ita ta fara mata tawaye yau gashi mariah me mata biyayya kamar kare da uban gidansa yau ta bar mata zauren ta akan dan abin da bai taka ƙara ya karya ba.. "wato Sultanate itama zata fara miki hawan kawara kenan kamar Sultanah karama?" Wani irin bacin rai Sultanate ta ji ya tsaya mata a rai ta juya tana murmushin yake ta ce musu. "A'a tana da nata uzurin dai. "Allah ya kyauta amma meye na hada Ummu Mansurah da wancan figaggiyar yarinyar? Yarinyar da tsabar girman kai ba, baka isa ta gaishe ka ba." Ba wani abu Hajiya Mariya tayi ba, amma yadda ake ririta zancen sai ka rantse da Allah ta zagi Sultanate ne. A can bangaren Sultanah Badi'atul Noor. Shiri sosai take zata tura Abuturab can wurin Yayunsa su zauna can shi yasa zata hada shi da Zuwairah da kuma Jalilah, su tafi can su zauna tare domin kaf duniya bata da amintattun bayin da ta aminta dasu kamar mutane biyun nan. "Ummin mu ko zaki duba wannan kayan." Dubawa tayi kafin ta ce mata. "Eh yayi kyau, ki saka a cikin su. Zuwairah akwai sakon Maiduguri da aka kawo min mun yi waya da Mamar takwara tace tana son turaren wuta a kai mata, ki duba story akwai kayan a wurin ki gayawa Jalilah ta haɗa a cikin kayan dake wurin ta a saka a cikin kaya, kafin ya gama bautar kasar sa mun gama shirin mu" "shi kenan an gama Ummin mu" murmushi tayi tana kallon ta. 'ki kare Yaranki, kowama za a iya sayan shi da kudi domin cika musu burin su' d'ago kai tayi tana kallon Zuwairah da ta kusan barin falon ta ce mata. "Zuwairah!" Juyawa tayi tana faɗin. "Na'am" "Kina son kudi?" Juyawa tayi sosai musamman da taji zancen kuɗi. "Sosai ranki shi dade" "idan na baki miliyan goma me zaki yi da shi?" Dariya tayi sosai sannan ta ce mata. "Allah ya baki lafiya da nisan kwana, Yarana zan yiwa hidima." "Kenan zaki iya sayar da yardanki akan kuɗi?" "Subhanalillahi, Ummin mu ai amana ɗaya ce kudi kuma daban " gyara zama Sultanah Badi'atul Noor tayi tana faɗin. "Gashi ni an gaya min cewa kowa a cikin gidan nan ya fi son kudi sama da Amana taya zan yarda da ku?" Zubewa tayi akan gwiwar ta. "Sultanah wallahi babu wanda ya isa ya siye ni na miki butulci ki yarda da ni " ita kanta Sultanah bata san me ya kawo wannan zancen ba, sai dai bata jin zata iya shiru ne a kashe ta. "Tashi ki tafi " "mun gode " "Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana." Ta fada tana barin falon. A fada kuwa. Shigowar wani mutum karfaffe ga kuma tsawo alkyabar shi sak irin na Sultan Abdulrahman Dan Aliyu ne, niman wuri yayi ya zauna, yana watsawa mutanen fadar kallon banza. "Mtseeeeeew " ya ja tsakin da Sarkin bulala sai da ya zabura. "Hattara dai waziri zaka sha ukuba" "mtseeeeeew nayi." A zabure Sarkin Bulala ya mike, Sultan ya d'aga mishi hannu. "Kar ka d'aga mishi da ya ga kad'an me ban haushi." Kallon waziri sauran mutanen fadar suka yi cikin takaici suka ce. " Kai dai baka da hali wallahi" "Eh sai me? Ku kuma babu amfanin zama da ku a rayuwa da ni ke zaune a wancan kujeran dai na fille muku kai." Murmushi Sultan yayi yana faɗin. "Kyawun dan arziki ya gaji ubansa." Mikewa Waziri yayi yana faɗin. "Da ban gaji Ubana ba wani tsiyar ce? Kai Abdulrahman wallahi ban ki naga mutuwar ka ba." "Hattara dai" "kai yi min shiru Ja'irin banza, shi Abdulrahmanu wani kwarjini ne da shi, waye bai san mulkin kama karyan da ake ayi a masarautar nan ba? Kalla gara kayi murabus yafi maka zaman da kake akanka da matar ka baka maku adalci ba wani shegen zaka yiwa adalci. Gara mutuwar ka sau dubu akan rayuwar ka, matse ka bani hanya" "dogarai ku rufe kofar " juyawa waziri yayi yana kallon Dan masani, murmushi yayi sannan ya ce mishi. "Yahya Adekunle stop pretending ka fitar da kiyayyar ka zai fi maka rayuwa a cikin inuwa bayan kasan a kowacce rana konewa kake kai ku bani hanya" ya daka musu tsawa. "Waye ya gaya maka kowa mahaukaci ne irin ka?" "Ka tambayi Abdulrahman ya gaya maka yadda na tsalleke bala'i balle Hauka" yana gama fadar haka yayi tafiyar shi. "Sam Waziri Dawood bai da mutunci." Har ya kai bakin kofar ya juya tare da kallon Dan Masani. "Tabbas bani da mutunci, sai dai ni kaifi daya ne idan bana son ka, iya gaskiyar kenan bana sonka. Ban ga hadisi ba babu hujjar wanka da tab'o ba. Abdulrahmanu ka gayawa mutanen ka, su ajiye kiyayyar su akan ka, Ni damuwata kujeran da ake zaune akan shi. Allah sarki hala kafin na zo ya tsufa " ya dawo cikin fadar tare da shafa kujeran da Sultan Abdulrahman yake zaune akai. "Wai na tambaye ka?" "Yaushe zaka mutu? Na gaji da ganin ka zaune akan kujeran nan kafin nazo ya tsufa" "yaushe kake son na mutu?" Sultan ya tambaye shi a sanyayye, d'aga kafad'ar shi yayi cikin ko in kula da yanayin Sultan ya ce. "Duk lokacin da ya maka" sannan ya ɗan sunkuya kad'an ya d'aga murya. "Ku shaida duk ranar da Abdulrahman ya mutu ni Dawud zan zama sabon Sultan" ya fada yana d'age gira daya. "kana sakaci da Addu'a Ubangiji yana tare da masu addu'a shi yasa nake maka abin da naso kafin ka mutu. Ka kula da Rayuwar yaran manyan nan maza uku " daga haka ya kuma d'aga murya domin maganar da yayi, a can ƙasa ƙasa yadda daga shi sai Sultan suka san me suke fada. "kar ka damu ni ba zan kashe ka ba, amma ina gaya maka na Barka ne domin abotar mu na shekaru arba'in ya cigaba da tafiya. Amma ka sake ka cigaba da tafiya haka babu wani sauyi juyin mulki zan maka " daga haka ya juya abin da ya bar fadar. Shiru fadar ya dauka kowa da abin da yake tattaunawa a ran shi. "Sultan yanzu shi wannan mutumin babu wani abun da za a mishi ne?" Inji dan masani. "Babu abin da zai masa, bayan abotar su na Yarinta har girma, Dawud yana abin da ya gadama." Murmushi Sultan yayi sannan ya ce musu. "Ku mishi uziri " "ai shi kenan uzuri kam ana mishi kullum sai dai rashin mutunci har yau bai daina ba, kuma baya jin zai dai na idan ya cigaba da wannan yanayin tabbas zamu dauki mataki akan shi. Tunda farko muka so koran shi ka hana mu" mikewa yayi fadawa suka mike tare da saka masa babban rigar su, suka rufe shi har ya bar fadar. A can cikin gida kuwa, Waziri Dawood wucewa wurin Sultanate yayi Dama sau uku yake shigowa duk karshen wata. Yana zuwa wurin Sarki ya mishi rashin mutunci, sannan yazo wurin Sultanate ya gaya mata bakar magana, da rashin arzikin, kafin ya wuce wurin Sultanah karama suyi hira sosai, wannan karon Sultanah Badi'atul Noor ce ta tura mishi sakon yazo don Allah tana son ganin sa. Kaf duniya Sultan bai da abokin da ya wuce Waziri Dawood abu daya ya raba amintar su. "Assalamu alaikum, Allah yasa gidan da Mala'ikun rahama, domin idan datti ya cika ya tumbtsa babu abin da ba za ayi aikatawa ba." Gabanta ne ya fadi, kaf cikin masarautar babu wanda yake mata abin da ya gadama kamar Dawud, "Wa'alaikumunsalam, lale maraba da zuwan mara kunya" "ina zan yi kunya tunda muna da irin ku a cikin masarautar nan, me zai hana ki daina bawa Badi'atul Noor ciwon kai ki fadawa duniya abin da kike aikatawa nasan zaki shiga kundin masu bajinta ta duniya" "Dawuda kenan an gaya maka kowacce magana ce ake fitar da ita? Ko an gaya maka dabi'ar ka shi zai saka na yi yadda nake so?" "Ko daya bana fatar haka, sai dai ni akwai wata.. 08130269641 [22/05, 3:03 pm] usmanlauratu71: 16 Sai dai akwai wata yar tantama da nake akan ki, kuma nasan wacece ke zaki iya aikata kome wallahi, na tausayawa Abokina da bai san irin uwar da yake tare da ita ba wallahi." Mikewa tayi ko ciwon kafarta bata tuna ba, ta ce mishi. "Zoka fita min a gida " "Bafa inda zani" tsaki tayi cikin fada da sababi ta ce. "Ban da rashin kunya da rashin girmama na gaba, taya kana dan kanwata kana gaya min abin da kaso" "don ina dan kanwarki sai akace min kar na gaya miki gaskiya, kin ga ku gaya musu ta yadda aka yi Mansurah ta mutu, domin wallahi na san kome. Kamar yadda Mutuwar Dawlat khatoon da danta, da mutuwar Abdulsamad da lalacewar Abdulrashid. Ko na fita na gayawa mutanen gari ne nace musu an raba Yaran Badi'atul Noor ne da sarautar nan gudun kar su gaji mahaifin su " wani irin zufa yake karyo mata bakinta yana rawa ta nuna shi da yatsa tana faɗin "Zargina kake?" Hada hannun shi yayi yana me kallon ta ya ce. 'ki kwantar da hankalin ki, na san wadanda suka yi kisan kuma kema kin sani me yasa kike zunguro inda yake damun mutane? Sannan meye laifin Yaran Badi'atul Noor?" "Halin ta ya shafi Yaranta." Ta fada tana juya kanta. " Shi yasa aka yi yunkurin kashe Aliyu?" Wani irin zabura tayi kamar zata fado kasa. "Me kake cewa ne? Wancan dan banza zasu kashe kuma? Me ya tsare musu naga dai ana binciken akan mutuwar da ake zargin shi yayi?" Mikewa yayi tare da saka hannu a cikin aljuhun babban rigar sa y ce mata. "Nasan ranki ya ɓaci ba? Bai kai na yadda kuka jefa Badi'atul Noor ba, wanda nasan matukar kuka cigaba da wannan tafiyar wata rana zata fito fili ta kalubalance ku, a lokacin shi kansa Abdulrahman bai da cikakken karfin kare ki da wannan nake baki shawara ki ajiye yakin ki a gefe shi kuma Abdulrashid ki daina lalata Mishi rayuwa bayan wanda aka san anyi na baya, babu adalci a rayuwar gidan nan. " daga haka ya juya ya bar falon, kasa zaune tayi ta kasa tsaye, asali yau Dawuda ya bata mamaki tabbas Dawuda yasan sirrin ta, da abin da ya dangance ta. Wayarta ta dauka. *** After two weeks. A gajiye take tafiya, kamar bazata iya tafiya ba, ga jakar makarantar da ya mata nauyi. Da sauri Rahilah ta amshi jakar tana mata alama sannu da hannu. Hawaye ne ya zubo mata. Har suka isa hostle kuka take, karshe ma bata ci abinci ba, da azhar yayi suka tafi masalaci acan ta cigaba da kwanciya. Abin da ya faru kuwa wata prefect ce ta shigo ajin, dake bata gani sai da madubi, shima ido daya ne yake gani dayan kan baya gani baki daya, tana shigowa ta isa gaban desk dinsu. Shi ne ta fitar da ita suka fita. Ko a ina ta samu labarin ta oho, ta wuce da ita hostle dinnsu, ta kwashe mata kayan abinci, sannan ta saka makafi yan uwanta suka zane ta. Tun da ta gane haka shi kenan, kullum sai ta saka an kawo mata Sa'ade ta zane ta. Tsoro yasa duk suka kasa kai karar ta, karshe yau da abin ya ishe ta ne ta gayawa head girl na bangaren su kurame. Kamar ta watsawa wuta fetur. Ita head girl din ta samu wancan Prefect din da magana, shi kenan fa yau da ya zama asabar bayan su fito da extral class, suka rufe ta da duka, kamar sun jaka. Suna cikin haka ne wani daga cikin dalibai maza ya shigo makarantar ta katanga. shima kurma ne, ya leko sabida yadda yaji Rahilah tana ihu da wasu irin surutu na kurame. Ya leko idanun shi ya tsaya akan yan matan, tausayin Sa'ade da suke zanewa tasa shi saukowa bayan ya karyi bulala, ya nufi cikin makarantar mata da shi, basu san da zuwan shi ba, sai jin saukar bulala suke. Ta ko ina, abin da ya firgita su kenan, suka juya da gudu. Ya d'aga sa'ade ya karkad'e mata kayan ta, sannan ya kira Husnah Jafar Kurmi wacce tsoro ya saka ta boya. Tambayar yayi da hannu. Hannunta ta kai goshinta. Sannan ta hancinta ta kuma hada hannun, "Bata mata kome ba, tun ranar laraba take dukarta kullum idan aka tashi break" "Da gaske?" Ya tambaye su, ya saka hannun shi tare da rike wuyar shi. Hannu Rahilah ta kai kumatunta tana faɗin. "Na rantse" lumshe idanun shi yayi ya bude akan sa'ade dake kuka har lokacin. "Ya isa ya mata alama da hannu. Haka suka nufi dakin su, suna jinjina abin. Wannan shi ne abin da ya faru a ranar, sai bayan la'asar suka dawo hostle. Sun samu jikinta da sauki ga kayan abinciin ta sun kashe tass. Zama suka yi, suka jika musu garin kwaki jika. Rahilah ta kawo Sugar, Ita kuma Sa'ade da ta ji dadin jikinta ta kawo gyada da kuli kuli ta mika musu, ta koma ta kwanta. Suka yi tasha amma fir taki sha, haka suka zauna har lokacin magarib yayi suka tafi masalaci basu dawo ba, sai isha shina wucewa wurin amsar abinci suka yi. Ina ko loma daya Sa'ade bata ci ba, sai amai, dole aka wuce da ita clinic, aka saka mata ruwa domin tayi weak, sannan aka kira coper Sadeeq aka gaya mishi, a daren ya kira Abuturab, wanda ya ke can ya saka Malam Aminu a gaba da Tsokanar sai ya biya shi kudinsa. Ya dauka, sun yi magana sosai sannan ya ce gobe dai shigo. Ita kuma a cikin clinic din ta kwana, Yarima Sadeeq ya koma. Rahilah da Husnah a wurinta suka kwana. Kowannen su kamar zai shige jikinta ya saka ciwon a kansa domin baki daya tausayinta ya narke musu a zuciya. Anan suka kwana da sassafe sai ga Abuturab. Abin dariya kamar mayu sun manne a gado daya, sun saka ta a tsakiyar su, suna barci. Rigar jikinta ne ya kware har saman sili-silin cinyarta ya ga shatin bulala, muryan Sadeeq yaji, da sauri ya janyo rigar ta rufe mata cinyarsa. Ya juya Yana kallon shi. "Man ya dai?" "Akwai masu cin zarafin ta a cikin makarantar nan?" "What'?" "Abin da na gani ne bari su tashi." Zuba musu idanu suka yi har suka tashi domin kansu, sai lokacin Rahilah ta tuna basu yi sallah ba, suka fita da gudu suna masu jin kunya sosai. Kallon Sa'ade yayi ya zauna a kujeran dake gaban gadon ya kalli karin ruwan ya kare. "meke damun ki?" Tashi tayi zaune tare da riko hannun shi. Ta mishi alama da hannu. "Don Allah ka kai ni wurin Innata, na yafe karatun zan je nayi kiwon yar tinkiyata" ta gaya masa. Dafa goshinta yayi sannan ya mike, kallon Sadeeq yayi sannan ya ce. "Ka gayawa shugaban makarantar na tafi da ita jinya." "Ok ba damuwa " fita yayi can sai gashi tare da mataimakin shugaban makarantar, sannan aka aka tura kiran su Rahilah suka kawo mata kayanta kala biyu. Kafin suka bar makarantar tana kuka su Rahilah suna kuka saboda shakuwa. Bai tsaya da ita ba sai wani babban private hospital a cikin garin Sokoto, suka shiga bata kulawa na musamman. Sai lokacin ya kira Zakaria, sun zo asibitin domin anan suka wuni shi da Yusuf, bai gayawa Aunty Ummi ba, sai da aka sallame su ta gansu da Sa'ade. A hankali ta zube a saman kujeran falon baki, ta kwanta kafin wani lokaci barci yayi gaba da ita. "Ni zan tafi sai gobe zan zo na ganta." "Tow Allah ya kai mu, mun gode sosai." Haka ya tafi yana jin babu dad'i. Washi gari monday karfe bakwai a makarantar ya mishi. Inda ya sa aka kira Rahilah da Husnah ya tambaye su me ya faru. Basu boye mishi ba suka gaya mishi abin da ya faru. Ya tsaya suka yi magana da shugaban makarantar, sannan aka kira yan matan. Suka zo tsoro yasa suka amsa abin da suka aikata. "Kun san me? Ai nasan kuna jina, wallahi billahi azim na kuma kama wata da laifin tab'a Sa'adatu Aminu Fulani, sai na karya yarinya. Shegu marasa kunya masu bakin ciki har cikin zukatar su. Waye bai sai halin ku ba. Look wannan ya zama deal dina da su, next time na kuma haduwa da su, kun gama karatun nan wallahi, ku ko zuciya baku da shi sai tsabar hassada da Kyashi na kuma zuwa ko a kirani kun taba daya daga cikin yara ukun nan sai na d'aye fatar ku na fasa muku kun cinye fitinanun mutane." Fada yake inda ya shiga ba tanan yake fita ba, abin ya bawa Sadeeq mamaki domin a sanin shi mutum ne da bai cika fada ba, kuma gashi nan ya zo yana bala'i kamar zai make su. Sake baki yayi yana kallon shi, yadda ya rufe idanun shi yana bala'i, sai bashi hakuri principal yake domin bai tab'a ganin masifaffen mutum irin shi ba, har ya gama masifar shi hakuri suke basa. Daga nan ya mike. "Ka shiga tsakanin su idan ba haka ba, kowacce sai na hanata sakat. Haka yayi ta gyada kai. ** Da yamma wurin la'asar yazo dauke da kayan ciye-ciye. Zama yayi yana kallon yadda take karanta wani tarihi me suka na Hausa, ya kurawa fuskar idanu, wani lokaci idan tana yin abu kamar Mansurah, murmushi yayi yana kallon kalabar kanta, gashin har kafad'arta gashi gashin baki me sirkin ja, irin na asalin fulani. Amsa yayi yana kallon ta. Tura baki tayi tana kallon littafin. Ganin yadda yake kallonta ta mike tsaye tana niman tafiya ya mata alamar ta zauna, zama tayi tana kallon window waje. "Jibi zaki koma makaranta" zaro idanu tayi tana me girgizar kanta ba zata ba. Hannun shi ya saka a wuya" na rantse sai kin tafi don haka gobe zan zo muje kasuwa kawayen ki , sun gaya min an kwashe Miki abincin ki." "Ni ba zan koma ba na gaya maka, kawai a mai dani gida " ta fada tana fashewa da kuka. Kura mata idanu yayi. "Baki son kiyi karatu ne ki zama wacce za anan nunata a tvn " hawaye ne ya zubo mata. Ta gyada kai tana nuna tana so, ya gyara zama sannan ta ce mata. "Share hawayen ki" 08130269641 [24/05, 6:00 pm] usmanlauratu71: Da dan sassarfa ta isa hostle din su, bata yarda ta shiga cikin hostle din ba, amma tana iya hangota, yadda ta tsuguna a gaban locket ɗin su, dake an gansu tare babu wanda ya kawo wani ta'addin tazo yi, tana kokarin bude locker din kenan Rahilah ta isa kwanar su. A firgice ta mike tana zare idanu. Nade hannu a kirji Rahilah tayi tana mata wani irin mugun kallo daga sama har kasa. Hàdiye yawun tsoro tayi tana faɗa mata ita bata dauki kome ba, rab'a gefenta Rahilah tayi ta kuma rufe locker din, sannan ta juya tana watsa mata kallon banza ta nuna mata hanya. "kar nan kuma ganin ki a cikin mu, ki tsaya iya kanki." Hàdiye yawu tayi ta wuce simi-simi kamar wacce aka watsawa ruwan zafi. Sannan Rahilah ta tafi ya same su. *** Hajiya Daulah. Tsura mishi idanu tai, ta rasa abin da zata gaya mishi ko zata mishi ta ji dadin rayuwarta asalima irin mugun b'acin rai take ji. "Abdulhakim meye nufinka? Nace ban isa da kai ba ne?" D'ago kai yayi idanun shi jajjur. "Kiyi hakuri bani da lafiya ne shi yasa ban je ba" tabbas matukar takardun shi suka fito zai gudu ya bar Hajiya ba zai iya da rigimar ta ba, ta hana shi sakat. "Ka sani ina kallon ka ne, duk lokacin da ka cika ni zan bata mata ka rai" ta fada tana bubbaga hannunta a kasa. "Allah ya huci zuciyar ki" ya fada yana barin falon, ita kanta bata son tana mishi fada anyhow, dauke kai tayi tana son ta bincika ta ina ta gaza a kulawar da take mishi? Amma baki daya baya damuwa da ita kamar yadda yake damuwa da mahaifin sa. Tana zaune a wurin Afiyyah ta shigo a gajiye, zama tayi tana kallon Hajiya. "Hajiya naga motar Yaya. Yana sama ne?" "Eh yana can" da gudu ta haura sama tana zaune. "Assalamu alaikum, Ya Abdul Barka da dai. Dama dama" kallonta yayi cikin kulawa sosai. "Kina son wani abu ne?" Ya tambaye ta a sanyayye. "Hmm uhmm, dama akan Sophia ce ta ce na" "get lost" da sauri ta juya, "mtsew" ya kawar da kan sa. Da gudu ta isa falon. "Hajiya" kura mata idanu tayi domin bata son magana. "Sophia ce ta ce min" "wuce ki bani wuri bana son magana don Allah" daga haka ta wuce mai da hankalinta tv, wurin karfe shiga Taufiq ya dawo. A kofar shigowa suka hadu. "Ya Abdul ya kake?" "Lafiya muje sallah" "tab na gaji idan na farka cikin dare zan yi sallah amma yanzu wallahi na gaji, idan bayi yau ba zan yi gobe in sha Allah" ya fada yana shiga da goyon jaka a bayan sa. "Allah ya kyauta" ya fada yana dauke ajiyar zuciya, ya nufi hanyar masjid da yake jikin gidan su, bai da so gidan ba, sai da aka bayan isha. Tunda ya shigo ya hango su a wurin cikin abinci masu aiki sai kaiwa da komowa suke. Bai ce musu cikanku ba ya wuce abin sa. "Abdul" Hajiya Daulah ta kira shi. "Na'am" ya amsa yana juyowa baki daya. "Zoka zauna ka ci abinci" ta fada a tausashe, domin bata son yayi ta yawo babu abin arzikn a cikin sa. "Na koshi" ya fada can kasar makoshinsa. "Zo nan Babana " ta fada a raunane, domin baki daya yadda yake bata son abin da zai iya lalata mata shirinta na son yayi aure ba. Takowa yayi har inda ta nuna mishi ya zauna yana kallon abinciin. "Ci" ta ce masa. Babu musu ya fara ci. "Hajiya kin mai da Yaya Abdul kamar wani yaro" inji Taufiq yana dariyar shakiyanci, murmushi tayi tana kallon Abdul din da yake cin abincin kamar bai da hakora a bakin sa. "Nayi magana da hajiya Nazirah akan Sophia ko zaka fara zuwa ne?" "Kwat" ya hàdiye abinciin bakin sa, yana kallon ta. "Baka fahimci me nace ba ne?" "Na fahimta " bata bar shi ya sake wani magana ba, domin ta lura da magana a bakin sa ta mike tana cewa"Allah ya taimaka ya daidaita kanku" "Amin" ya fada muryan shi yana rawa. Dauke kai tai tana haurawa sama, tana halkance da shi, yadda yake kallonta. Amma bata jin zata iya kyale shi. Tana barin wurin ya mike shima ya nufi waje, yana shan iska baki daya kome ya tsaya mishi cak, bai da wani kuzarin da zai fadi abin da yake damun sa, tare da fadar likita yace saboda ciwon shi ba zai iya zama da mace ba, tunda shi ciwon haihuwar shi aka yi da ita ba daga sama ya same ta ba, domin da daga sama ne tabbas da yanzu yana da mata da yara kamar kowa, kuma abin da yake kara dagula lissafin sa, shi ne har yau bai da wacce zai nuna a matsayin yana so asalima har yanzu bai da cikakken lokacin da zai kalli mace domin kansa. Sai dai ya musu kallon tsoro ya wuce. Shigowar motar Dr Sharif wato mahaifin su. Mikewa yayi ya nufi wurin sa, ya jira sai da yayi parking sannan ya kashe motar ya fito, amsar jakar hannun mahaifin su yayi yana faɗin. "Barka da zuwa." "Yawwa Abdul Hakim ya na same ku?" "Alhamdulillahi" ya fada suna jerawa, "Ya Aunty Faridah?" "Tana lafiya sun ce na gaishe ka" ya fada yana kallon sa. "Kana da damuwa ne ?" "Na'am" sai kuma yayi yar murmushi, sannan ya sosa kansa. "Ba kome" ya fada yana tafiya ciki da sassarfa. "Abdul Hakim meke damunka?" "A'a babu kome" ajiyar zuciya Dr Sharif ya sauke tare da bin bayan sa. Dakin Abban su ya kai mishi kayansa, sannan ya wuce dakin su, a duk lokacin da Mahaifin su yake gidan yana jin wani irin kwarin gwiwa da ita yake kwana, sai da Dr Sharif ya huta sannan ya wuce dinning table ya ci abinciin sa. Sannan ya wuce dakin Hajiya Daulah. Hankalinta yana kan wasu takardu ya shiga ya ja kujeran mirror ɗinta. Ya zauna yana kallon ta, "Ranki shi dade zaki bani aron lokacin ki?" "Emmm!" Ta fada hankalinta yana kan takardun, "ina son ki ajiye kayan gabanki muyi magana akan rayuwar Abdul Hakim" sai lokacin ta ajiye takardun ya zuba masa idanu. "Ina jinka" tattaro nutsuwar sa yayi ya kalle ta sannan ya ce mata. "Abdul Hakim ba zai iya zama da mace ba, duk yadda kike son yayi aure na fiki kaunar haka, domin har auren yar Sultan an bashi, ba na gaya miki haka ne domin ki d'aga min hankali ba, na gaya miki ne domin ki san matsalar d'anki, ba zai iya zama da macen da kike ra'ayi ba, likitan shi ya tabbatar da matukar shi yaga mace yana so tow zai iya zama da ita kuma idan tana son shi zata zauna da shi, ba auren dole ba." "Kana nufin zan matsa mishi yayi aure ne? Ko kana son cewa na takura mishi da zancen aure?'" "hmm" yayi murmushi me sauti yana kallon ta, kafin ya ce mata." Ko daya ina son ki tuna da cewa shi din amana ne Allah ya bamu tsakanin mu da shi akwai hisabi kar ki yi abin da zai tsaya a gaban Ubangiji ya nima mishi hakkin sa, don Allah kar ki tsannanta mishi, mu kyautata mishi gani nake kamar duk halin da yake ciki mune sanadin haka, don Allah ki yi haquri." Kamar ta rufe Dr Sharif da duka, amma haka ta rufe idanunta ta, na tsawon minti goma sha biyar, kafin ta bude fuskar ta yayi jajjur Idanunta sun kankance domin takai matukar bacin rai, jan drower gadon tayi ta zuba takardun ta cigaba da kallon Dr Sharif, a hankali tayi murmushin karfin hali, ta ce mishi. "Zaka iya tafiya kaina yana ciwo" gyada mata kai yayi domin har ga Allah baya son tashin hankali su ya shafi Yaran su, shi yasa yake mata biyayya kamar ita ke auren shi ba shi ke auren ta ba. Haka ya fito jikin shi a mace ya wuce dakin sa, itama kuma kashe wutar dakin tayi tare da ƙwanciyar ta, amma ba barci tayi ba, sai dai tana saka abubuwa masu yawan gaske akan danta da mijinta, tana son Abdul yayi aure tana son ganin jinin sa a duniya. Ba haka kawai take takurawa ba, Yes tana son ganin sa cikin farin ciki da walwala. *** Few weeks ago. Saturday visiting. Tun safe suke shiri sosai, kai ka rantse da Allah sun shekara basu ga iyayen su ba, idan ka cire Rahilah da take kwance. Sa'ade anyi wanka Umma metro ɗin su, ta musu guga, sai sheki check dinsu yake, ita da Husnah, Kubrah tana rabe a gefe, duk da basu san me yasa take kin zama a cikin su ba, amma haka suke janta cikin su, inda tayi kokarin hana kanta daukar kome nasu, sai na sauran yan room ɗin, idan ana sururun anyi sata, kallo daya Rahilah ke mata ta shiga kame-kame. Dukar pillow da Rahilah take kai Sa'ade tayi, ta bude idanunta da suka yi jajjur. "tashi mu tafi kin ji" ta mata magana, saka hannu tayi a wuyarta ta ce mata. "Bani da lafiya ne" kallon kuru tayi mata, tana son hango iyakar gaskiyar Rahilah, "shi kenan" ta fada suka fita suna mata fatan Allah ya ba ta lafiya, har sun yi tafiya me nisa, sa'ade ta kalle su musu alamar su tafi tana zuwa. Ta juya abin ta, kallon ta suka yi. Kafin kamar hadin baki suma suka biyo ta, ana ta fita a room ɗin ba kowa, sai Rahilah da take zaune tsakiyar gadon tana ta rusa kuka, wani irin maraici da kewar Iyayenta take ji, bata da d'an uwa ita ɗaya suka haifa suka rasu baki daya, yan uwan Baban ta, ba zuwa suke ba, sai dai Aunty ta aiko mata garin kwaki da sugar. Yadda ta cusa kanta a tsakanin cinyarta tana kuka sai yq taba zuciyar duk wanda ya iso in da take, zagaye ta sukayi suna kallonta. Kafin Sa'ade ta dafata, a tsorace ta d'ago kai. Ganin Sa'ade ne, fadawa jikinta tayi tana kuka. Itama kuka take, abu daya ya tsara da kukan su. Shigowar Umma ta saka salati tasan ba wani ji suke can can ba, sai da ta matsa kusa da su, ta musu dakuwa tare da musu al'amar su tafi ana niman Husnah Jafar Kurmi, amsawa Husnah tayi, ta mikawa Rahilah kayanta, suna tsaye har ta shirya, a hanyar tafiya suka gamu da wasu senior sun zo niman Kubrah, Iyayenta sun zo, sai da suka fara zuwa wurin iyayen Husnah, suka gaishe su sannan suka wuce wurin iyayen Kubrah, kallon Kubrah suka yi domin basu ga a lamar Maman ta ba, sai dai da alamar matar da mijinta da dan su daya, matar tana kama sosai da Kubrah, itama bafulatana ce, komawa bayan Sa'ade Kubrah tai jikinta yana rawa, juyawa suka yi suna kallon ta. Hawaye na zuba daga idanunta. Dake dukkan su yara ne babu me hankalin da zai iya cewa wani abu ne, Yarima Sadeeq da Abuturab suna hango su, daga can wurin class. "Me ka fahimta?" "Kai dalla kawai dai bata yi appreciate da zuwan su bane" "har yau baka son kome akan masu matsalar nakasa ba, kaga lokacin da suka tawo, da gudu yarinyar ta isa wurin matar, ganin mijin yasa ya fara ja baya. " "Case closed don Allah kayi naka matsalar" Abuturab ya fada, domin baya son magana, idanun shi na kan Sa'ade da take bubuga bayan Kubrah. Takowa mijin matar yayi, ya cire hannun Sa'ade ya fara kokarin janye ta jikin sa, da karfi ta fashe da kuka. Ya juya ga Yayarta yana kallon ta irin kallon shu'umancin nan ya fara magana. "Salmah ba zaki mata magana ba." Jikinta yana kerma ta mata alamar ta daina ihu. "Ki gaya mata bana son ganin yaran nan a tare da ita ko na dauki mugun mataki " ya fada yana shiga gaban motar, sai kallon su ake, haka ta shigar da Kubrah motar, da aka saka mishi tintak. Sauke glass din motar yayi yana bin su da mugun kallo, a mugun tsorace suka juya, kamar zasu kifa. Musamman Sa'ade da ta hango tsanar su a fuskar shi. Hango Yusuf tayi yana nimansu, da gudu ta isa wurin shi dake ya basu baya, ta ja rigar shi. Juyawa yayi ta fada jikin shi tana murna. 18 Hakkin Mallakar Mai_Dambu 08130269641 [26/05, 5:07 pm] usmanlauratu71: Rike ta tayi yana dariyar farin ciki, juya baya Abuturab yayi, yana shafa kansa. Da mamaki Yarima Sadeeq ya ce mishi. "Ya ka juya baya?" "Uwar me gabana zai maka" ya tambaye shi, a hankali. "Allah ya huc zuciyar ka. Ai ba don Yusuf dan uwanta ba ne da zasu dace idan ta girma" take kafar Sadeeq yayi da karfin gaske. Sai da yayi ƙara. "Watch your tongue" "daga fadar gaskiya" "Mtseeeeeew" Abuturab ya ja tsaki, "Malam meye najin haushina?" Share Sadeeq yayi yana kallon Sa'ade da yan uwanta da Mamanta. "Baka san Arzikin da yake cikin sanya mutane farin ciki ba ne? Da ka sani ba zaka dame ni da wani batu na daban ba." Ya fada mishi yana saka madubin sa na no respect. Wurin su ya nufa, yana isa wurin "Assalamu alaikum " ya musu sallama yana kallon ta, ta cikin madubin yadda take kara narkewa a jikin Innarta. "Gadanga kusar yaƙi, ka zo ne?" Inna Laminde ta fada tana murmushi. Zare madubin yayi yana shafa kansa. " "Eh Inna, an zo wurin auta kenan?" Dake a Husnah ta na wurin Iyayenta, Rahilah tana tare da Sa'ade, amma hankalin ta yana kan motar su Kubrah da ta bar harabar, kallon Sa'ade tayi tare da gaya mata mata magana. "Motar su Kubrah bata nan fa!" Leka wurin tayi itama. Da sauri ta mike a jikin Innarta, suka bar wurin. Abin ka da Yaranta suka tafi wurin Husnah da take hira da kannenta, ganin yadda take cikin farin ciki yasa suka barta suka tafi. Abuturab yana kallon su. Sako ya turawa Sadeeq. *Ga yaran nan ka bibiye, zasu ta wurin kawarsu* a can motar kuwa, tunda ya bar cikin mutane, ya saka yayar Kubrah ta fito waje, ya koma bayan. "Wato ke me taurin kai? Bana ce babu ruwan ki da kowa ba? Har zaki fara nunawa mutane ina miki wani abu" girgiza kai tayi tana kare fuskar ta, haka ya murde hannunta yayi ta kifa mata mari, kafin ya kai hannun shi cikin rigar ta kuka take tana, kare fuskarta. Itama Salmah da take gaban motar kuka take, domin tausayin yar karamar kanwarta. Sai da ya ga ta daina kuka tana ajiyar zuciya sannan ya ce. "fita ki bani wuri, zan mata fada." Fita tayi da danta. Hawaye na zuba mata, hannun sa ya kai bayan Kubrah, yana shafa ta a hankali yana faɗin. "Idan kika min abin da nace, zan daina hana Salmah abinci, amma idan kika ki yi min yadda nace, wallahi sai dai ta fara sata kamar ke." Gyada mishi kai tayi, d'aga rigar shi yayi, jikinta ya shiga kerma, ganin yadda ta boye fuskartar tana shashekar kuka yasa shi damko gashin kanta, ya kai tsakiyar cinyar shi. Ya danne kanta tare da tura mata kukanbanba dinsa, buga kofar motar aka yi da karfi dai da ya razana. Cikin takaici ya hango Rahilah tana buga kofar, Ita kuma Sa'ade tana wurin Salmah a fusace ya maida wandonsa, ya bude motar a hankali tare da tokarar motar, sai da Rahilah ta fadi can, ya fito idanun shi jajjur. Da gudu Sa'ade ta d'ago Rahilah, tana leka motar, a hankali ta sunkuya kamar me niman wani abu, kawai yarinyar nan ta dibi kasa ta watsa mishi a idanu, da gudu suka bude inda Kubrah take, suka juya da gudu suna barin wurin, karo suka yi da Abuturab. Musamman ita da ya koma zata fadi. Mijin Yayar Kubrah da yake ta ihun sun watsa mishi kasa a idanu, dakyar ya share idanu Salmah ta mika mishi ruwa, ya wanke idanun shi, yana fara gani ya kifa mataS pp mari, sannan ya bi bayan su. Bai gansu ba sai da yayi ta niman su, kafin ya hango su Abuturab yana tsaye da Inna suna magana ta mika mishi wani farin gora cike da madara, dafaffiya. A hankali idanunta ya hango mata mijin Yayan Kubrah dauke da wani katako, tsabar ta rikice bata san lokacin da ta ture shi ba, katakon ya sauka a gefen kafad'ar Abuturab. Sake rikicewa wurin yayi da ihu, da sauri Sadeeq ya kai mishi dauki, duk da ba wani abu ba ne. " Sake ni naci uban sa." Principal da yan sanda suka iso wurin. Zare idanu yayi yana kallon Kubrah da gefen fuskartar yayi jajjur, sai fuskar Salmah da ta yi ja shima. "Officer kuyi arrested din shi," inji Principal, "Meye nayi? Me na muku?" "Kai yi mana shiru muje zaka ji abin da kayi" "Aliyu da fatan babu matsala ko?" Principal ya tambayi Abuturab. "Ba kome" "Allah ya tsare na gaba, mun gode da taimakon da ka mana, ita yarinyar zamu kira social warfare su shiga al'amarin da kungiyar su na Handicapped su tsaya mata, mun gode sosai" "ba kome ni dai fatana, yaran su karatu " gyada kai yayi yana faɗin."in sha Allah " bayan tafiyar Principal ne su Yusuf suke tambayar shi ne ya faru. Sadeeq ya basu labarin abin da yake faruwa. "Yallabai da Fatah babu abin da zai samu Sa'ade?" "In sha Allah babu, sai ma fatan Alkhairi da zamu mata, domin tayi kokarin." Ya fada yana kallon ta. Yadda suke cure wuri guda. "Don Allah kar ki ji tsoron kome, ki fadi gaskiya a wurin Hukuma zasu karbar muku hakkin su." Sadeeq ya fadawa Salmah da take ta kuka. Domin tsoro ne da ita kamar farar kura. Haka ta fito da kayan da tazowa Kubrah da shi suka yi ta shigar da su, har na Sa'ade da Husnah, sannan suka fito suka yiwa iyayen su Sallama, sai da Inna ta raka Salmah gidan ta tare da su Abuturab, ana suka samu mahaifin su Kubrah yana ta fada. Lokacin da Abuturab ya isa wurin shi kallon shi yayi kafin ya ce mishi. "Dattijo kaga wannan saurayin? Dan Sarkin Musulmi ne, idan yaso zai iya kai karar ka wurin Mahaifin sa kana kare mai laifi bayan mutumin nan, zalunci yake, Salmah ka aura mishi ko kubrah da zai lalata mata goben ta?" Cikin sassauta murya tsawon ya ce.Yaro baka san halin su ba ne, ita fa Kubrah sace-sace take mana shi ya sa ya dauke ta " "Eh tabbas tana sace-sace, amma waye ya sanadin? Kai da matan ka. Domin da mahaifiyar Kubrah tana raye ba zata barta da yunwa ba, ba kuma zata wulakanta rayuwarta ba. Saboda marainiya ce babu uwa kai da zaka zame musu uwa Uba ka kyamace su, ita kanta wannan tana tsoron fadar gaskiya domin kar aurenta ya lalace, Alhaji duk wanda ka gani da abin da Allah ya nufa akan su, don Allah ka rike kyautar da ya baka, yana sane da su. Bance sai shiga al'amarin aurenta ba, amma kasan hukuncin auren akan mutumin da yake niman Ya ya nime kanwa. Rayuwar Yaranka mata, nasan kana da wasu yaran amma kome lalacewar su, wata rana sunanka sai ya fito don Allah ka kula da su, idan da dama ta hakura da auren tayi karatu miji na gari zai zo" wani irin abu yaji ya tsaya a kan sa, hawaye ya shiga zubo mishi. "Na gode zan kula sosai. Shi kuma Fa'iz yaje na bar shi da Allah zai saka mana " "Amin Ya Allah, Alhaji kayi hakuri amma yaron nan ba zai tab'a barin wani ya cutar da ita ba, ka rungume su itama ta rungume danta domin wata rana ayi alfahari da su. Zamu tafi" inji Inna. "Alhaji don Allah ka toshe kunnenka Yaranka rahama ne a gare ka, kar ka ki su." Sun bar gidan zuciyar su sawai, domin mahaifin su Kubrah kamar wanda ya farka daga mafarki, haka ya nunawa Salmah dakin ta, dama su biyu ne mata, tun rasuwar mahaifiyar su kome ya lalace matar sa muguwa ce, kaninta yake auren Salmah Fa'iz, baban su Kubrah yana da rufin asiri sosai domin dan kasuwa ne da yake da manyan shaguna Central market sokoto, Fa'iz yake rike da wasu shopping complex ɗin sa. Domin matar sa ita ta sa ya bawa kaninta auren Salmah domin su kwace dukiyar sai Allah bai nufa ba, domin mutum ne da yake da lissafi, kuma abu daya da suka kasa yi akan sa shine yana da yawan ibada, sun gaza nasara a kasan sai suka raba shi da Yaransa musamman Kubrah, da ita kan an san uban yana matukar tausayinta, shine aka jona mata sata, kamar bera abin haushi ko ta dauka bata iya cin ko tayi amfani da shi sai ta ajiye yadda za a kamata, wannan yanayin matar uban ta saka shi a gaba sai da Fa'iz yazo ya amshe ta, kamar da gaske shima ya daura nashi zalunci, gashi dukiyar ubansu yake lalatawa amma basu da ikon cin abinci sai ya basu, kai ga wani mugunta da yake na son lalata Yarinyar, dakyar ya kawo ta Makarantar inda ya mata kashedin kar tayi kawa ta zauna a hka. Sai gashi tayi kawayen masu tausayi. Domin kuwa daga baya Rahilah ta saka idanu akan ta, babban abin da yake bata mamaki idan yayi Sata bata ci, zata bar shi a wurin. Haka yasa sau goma ta dauko Rahilah zata ma maidawa masu shi. Kayan su, sai dai a gama masifar anyi sata daga baya a samu, domin tasha ganin tana kuka idan tayi abin, zaman su gashi nan dai kusan tausayin junan su, suke.. ** bayan barin su Abuturab daga unguwar su Kubrah. Suka isa kan wuri, sai da ya huta ya bawa Ummu Hafsah madaran, ya kira Ummin sa, tashi yayi ya fita daga cikin gidan ya nufi can harabar gidan ya zauna. "Ummina wai meke faruwa ne? Kin sani a duhu baki ɗaya?" Ajiyar zuciya ta sauke me nauyi kafin ta ce mishi. "Allah yayiwa Mansurah rasuwa" wani irin dauke wuta yayi, a hankali yaji kamar wani irin iska me karfi tana fisgar shi, duhu me karfin gaske ya lullube idanun shi. Daga can nesa yaji ana kiran shi amma ina tafiyar tayi nisa, a wurin ya zube ba tare da yasan waye a kan sa ba. Masu hidimar harabar ne suka hango shi a kasa, babu bata lokaci aka sanarwar Sadeeq suka nufi asibiti da shi. Sai da aka ɗauki tsawon lokaci kafin aka samu kansa, sannan aka mai da shi wani daki ya huta, har dare Aliyu be farka ba, washi gari Ba'aditul Noor da Rumaisah tare da Ummu Aymana, suka iso hankalin su a tashe. Har zuwa lokacin bai farka ba, Ita kan Ummi Addu'oin tare da sallar nafilla, shi tayi tayi tana gayawa Allah kukanta. Wasa wasa Aliyu ya kwashe kwana biyu bai san waye ma akan sa ba, sai a kwana na uku da yamma domin suna fadar cewa zasu mai da shi Kwara, Allah da ikon shi bayan salla la'asar, ya bude idanun shi. Lokacin Ummi tana lazumi computer din da aka saka mishi suka fara kara, shafa Addu'oin ta, tayi tare da mikewa tana me hamdalla, ta nufi waje ta cikaro da nurse din da suke duba bashi. "Alhamdulillahi ya farka" ta fada fuskarta dauke da murmushi. "Masha Allah, Autan Hajiya ya farka." Nurse din ta fada, suka nufi dakin, ta fara duba shi kafin ta kuma fita can sai Gasu tare tambayoyi ya fara mishi, yana bin shi da idanun, ya sake kallon Ummi ya ce. "Hajiya bai farka baki daya ba, amma idan ya farka zai gane komi." Shiru tayi kafin ta ce . "Ubangiji ya tashi kafad'ar shi." "Amin Hajiya ina jin dadin yadda kike nuna kwarin gwiwa akan shi." Murmushi tayi tana kallon Abuturab ..... Top-notch 08130269641 [27/05, 7:03 pm] usmanlauratu71: Duk da haka karfin hali ne, kawai da halin da yake ciki, domin har ga Allah tana cikin damuwa da tsoron kar wani abu ya same shi, zuciyarta yayi nauyi gani take kamar wani abu zai same sa. Amma shi never give up akan sa ta wani fannin. Wayarta ce tayi tsiwa, sai da ta kalli fuskar wayar tare da kura mishi idanu, kamar tana son hango wanda ya kirata, yankewa kiran yayi ta wani ya kuma shigowa, Kirjinta yana wani irin bugawa ta dauka, tana faɗin. "Assalamu alaikum" shiru daga can gefen aka yi. "Badi'atul Noor kina wasa da ni ko? Kina wasa da abin da muke yi? Hmmm kina tsammanin." Kashe wayar tayi tana faɗin"Innalillahi wa'inna ilahi rajuun." Ta lumshe idanunta, na wani lokaci kafin ta bude akan abuturab, ya gama zaman shi kawai ya tafi can wurin Yayunsa ya zauna kamar yadda ta shirya. Haka tayi ta sakar zuci har wani lokaci. Washi gari karfe tara na safe ya farka, bakin shi dauke da Ummu Mansurah, rike hannun Rumaisah tayi tana shafa kansa. "Kayi hakuri Allah da ya bamu ita ya amshi abin sa, kar ka." Kokarin tashi yayi ta ce mishi. "Auta kwanta ka huta " "Hatsari tayi ko ciwo tayi ta mutu?" Girgiza mishi kai tayi, "xan gaya maka amma sai ka nutsu" shigowar likitan ya sa ta motsa gefe, aka cigaba da duba shi, tsawon minti Talatin kafin likitan ya ce "a bashi wani abu, sannan kar a cika damun sa ya huta sosai" "in sha Allah babu me damun sa." Haka suka fita sai ga Ummi da yan gidan su Sadeeq. "Alhamdulillahi ya jikin sa." Sadeeq ya tambaya yana niman wuri ya zauna a kusa da shi. "Ummina ciwo Mansurah tayi?" "Amma auta baka ji likita ya ce ka huta ba." Lumshe idanusa yayi, "Maina rike shi ya shiga ban daki yayi wanka" haka Sadeeq ya taimaka masa, yayi wanka da alola, karfin hali yake amma bai ki yayi ta rusa kuka ba, haka suka fito ya gabatar da salollin da suke kansa. Tunda ya idar da sallah yake sauke ajiyar zuciya, idanun shi sun yi jajjajur. Jijjiyar goshinsa sun firfito rad'a-rad'a. Jikin shi sai rawa yake, dafa hannun sa Ummi tayi "Allah da ya bamu shi ya amshe ta, na meye tashin hankalin? Nasan kana sonta amma ba yana nufin zaka haukace akan ta bane. Tafi bukatar Addu'oin mu sama da tashin hankali ko kukan mu. Allah yasa dalilin haka. Don Allah kar ka kuma jifa kanka cikin wani hali" kura mata idanu yayi, kafin ya gyada kai yana jin kamar zuciyar shi zata fita. Wani irin tausayi kan sa yayi, sai a lokacin kome ya fara dawo Mishi tsawon wata uku da yayi. "Me ya same ta ta rasu, rashin lafiya tayi ko wani abu ne ya same ta? A'a ciwon cikin ne?" Hawaye ne ya zubo daga idanun Ummin ta ce. "ko daya, tsintar gawarta aka yi a bayan dakinka" mikewa yayi tsabar kidima , rike shi Sadeeq yayi. Ya durkusa a gaban Ummi har lokacin Sadeeq yana rike da shi, ya kifa kansa a kirjin shi. bata ga amfanin boye mishi ba, domin ko bata gaya mishi ba, ya gama zaman Nigeria balle kuma idan ta gaya masa ma dole ya bar ƙasar. "Zancen da nake gaya maka har an saka duk wanda ya ganka ya kashe ka, amma an janye kayi hakuri gobe zaka bar kasar domin nasa an gama maka kome sai tafiya." D'ago kai yayi idanun shi sunyi wani irin kankancewa. "Kina tsammanin dan ya saka a kashe ni zan tafi ne? Sai na nime duk wanda yake da hannu a mutuwar Mansurah ba zan barta jinin ta ya salwanta ba" ya fada yana mikewa. "Ba zaka tab'a zuwa ba, mu wuce na kaika lagos ka bar kasar nan a idanuna " ta fada tana niman fita, da sauri ya rike hannunta, yana haki. "Don Allah ki bar ni nayi facing shi please " yadda ta ga iyakancin kokarin sa na hana hawaye zuba daga idanunsu, ta fahimci he was mad, babu amfanin hana shi ya je din tunda yasan ba bar sa za ayi ya shiga cikin gidan ba. Don haka ta fita, zuwa tayi ta nima mishi sallama, and tayi alkawarin kare jinin shi da rayuwar sa. Haka kuwa suka basu sallama, daga nan ko Binji bai kuma tunawa ba, domin airport suka wuce. Sadeeq yana rike da shi ya ce mishi. "Me yasa ba zaka yiwa Sa'ade good bye ba" wani irin jiri ne ya nime zubda shi, yayi maza ya rike Sadeeq yana numfashi. "Ka ce mata zan zo" "when?" Girgiza kai yayi yana faɗin "Ban sani ba, ban san Yaushe ba, amma zan dawo ka gaya mata tayi karatu sosai, a duk inda nake ina kallonta." Daga haka yayi shiru, har lokacin tafiyar su yayi. Suka wuce cike da kewar juna, shi da Sadeeq. After few hours suka sauka a garin kwara, daga nan aka wuce da su har gida, sai dai abin takaici tun basu kai ga isa kofar get din ba, aka hana shi shiga masarautar. Haka su Ummi suka shiga masarautar babu shi, yana tsaye a bakin kofar gidan anan yayi Sallah azhar da la'asar, magariba a wurin bai matsa ba. Abinci ma daga gidan Ummul Aymana aka kawo mishi, wasa wasa har dare yana wurin a zaune, babu tsoro a ran sa ko fuskar shi. Sai bayan isha, Ummin su ta fito kana ganinta kasan tayi kuka har ta godewa Allah, ta zo inda yake ta ce mishi. "Mahaifin ku ba zai saurare ka ba, ka tashi maza na raka ka, gidan Ummu Aymana ka kwaka gobe ka wuce England" a hankali ya mike, Zuwairah da Jalilah suka kwashe kayan abinciin, suka nufi wurin mota da su. Har gidan Aymana suka kai sa, dakyar Ummi ta bar gidan, ko da bata gaya masa ba yasan sun sha rigima kafin ta fito. Koda ta koma ta sami Sultan Abdulrahman yana jiranta da bala'i, duk abin da yake bata magana, amma wannan karon tayi abin da ya bashi mamaki domin tsaf ta tsaya ta wanke shi, sannan ta bar shi ta gaji da abin da yake mata na rashin uziri, daren ranar bata yi barci ba, abin mamaki yadda zaka fahimci akwai muguwar sarkakiya a cikin masarautar, a daren ranar aka kai hari gidan Ummu Aymana, Allah yasa mijinta soja ne, kuma gidan akwai securitys da manya manyan police dog, sai dai anyi musayan wuta, tare da raunata wani soja, faruwan al'amarin ya tashi kan Sultan shi kansa tsoron al'amarin yasa babu shiri a wayewar gari ranar ya saka aka tura Abuturab England wurin yan uwansa, tare da rakiyar Zuwairah da Jalilah, aka bar Ummi da Mama hajja da Umma suwaiba da Hidaya, duk su din bayi ne a cikin masarautar, Ummi bata samu nutsuwa ba, sai da ta ga Abuturab ya shiga cikin jirgi sannan ta sauke ajiyar zuciya, ta san ya tsira daga sharrin masu kulle-kulle. ** A hankali rayuwar makaranta ya zama jikin yan mata uku, inda gefe guda Sadeeq bai baya mata sakon Abuturab ba, sai ma saka idanu da yayi a kan su. Yaran hudu Masha Allah, amma ta gefe guda Kubrah ta fi su shaidanci. Case dinta kuwa human rights sun dauki responsible ɗinta, inda suka maka Fa'iz a kotu, shi da Yayar sa, aka nimawa Salmah da Kubrah hakkinsu. Batun sata kuwa dukkan su sun san Kubrah na sata, sau dai suna kiyayye abin da zata dauka, rashin ji a cikin ta, kamar wacce ake kara mata shi. Sun fito shan iska kasacewar ana hutun public holiday, Sa'ade tana saman windown dakinsu, Husnah ta gefen tana wanke socks dinta. Sai tsaki take tana kwafa. Rahilah tana yanka tuwon madara da aka yi na jiya, domin dukkan su babu wanda ya ci, shi ne ta zubda miyar kubewa da aka yi, ta wanke ta ajiye musu, bayan ta gama, ta mike tare da daukar kofi ta wuce can kitchen, ta samo musu ruwan zafi, tana zuwa ta juye tuwon a cikin ruwan, ta rufe. Fitowa tayi ta dauki socks dinta da na Sa'ade, ta jika tana wankewa. Sai ga wata prefect, tana zuwa ta yi kwallo da bokitin Rahilah. Tsuru-tsuru suka yi, suna kallon ta, watsa hannu tayi cikin masifa tare da zagin su. Kallon juna suka yi, tayi ta bala'i tana zagin su, ku su dibo mata ruwa ko ta ci kutumar Ubansu. Zarar bokitin Kubrah tayi, bata ce kome ba, ta wuce dibo mata ruwan haka Rahilah da sa'ade. Suna isa burtsatsan, Kubrah ta wuce abinta baya ta ajiye bokitin, dajin cikin makarantar ta shiga, bishiyar da karara yake ta nufa, ta kuwa tsinko shi da dankwalinta, ta dawo, babu kowa a buhol ɗin, akan idanun su Sa'ade ta fasa kararan ta zuba a wurin, ta saka dukkan a cikin bokatayen, sannan ta daura musu dukkan su, nufi hostle tsakanin Rahilah da Sa'ade ba asan waye yafi wani tsoro ba, suna zuwa suka sauke juna, nuna musu toilet tayi suka kai ruwan, sannan suka koma dakin su, suka kwashe abinciin su, suka gudu. Domin sun san tabbas akwai Bidiri. Aikuwa Prefect din tana shiga ban daki, ta kwabe ita da Kawarta suka dauki ruwa suka fara cude jikin junan su. Sai da suka gama wanka tass, kaikayi ya ce salamu alaikum, tun a ban daki suke sosawa juna jiki, har suka fito, dake ana zafi, Bala'in tafi haka domin sai da suka yi ta watsi da towel dinsu, tashin hankali. Abinka da kurame ji kake ana "beebeee beeeebeee, baaaaa baaaa, aushhhhh" abinda suke fada kenan sai burgima suke kamar kan su zai fita, suna cikin haka Umma tazo. Nan ma sai da aka tafi har kitchen aka dibo manja da toka aka shafa musu. Dakyar kaikayin.ya tafi, ai kuwa suka sha alwashin zane su sa'ade, abin ka da yarinta. Da magariba suka dawo. Suna shigowa hostle din ana rufe kofar. Sai da suka zane yaran nan hankalin su ya kwanta. Dakyar suka shiga dakin su, Sa'ade nata kuka. Husnah ta ce musu. "Ya isa kuyi shiru, daga yau ba zaa kuma dukan mu ba, sai mun rama muma" kallon Kubrah tayi ta ce mata. "Ki shiga dakin Umma ki dauko mana jan bakinta, Ina da farin hoda" aikuwa ko rufe baki bata yi ba, Kubrah ta wuce dakin umma da take can wurin abinci a kitchen, ta dauko janbakin suka ajiye, sai da suka tafi masallaci, suka dawo dake ana zafi, haka suka dawo suka karbo abincin su, suka ci sannan suka bi sawun masu ƙwanciyar zafi, ana ta hira har aka yi shiru. Suka tashi baki dayan su, suka nufi dakin su, zanuwar gadon su, suka dauka kowaccen su, ta bude jikinta da hoda, bakin su suka bata da jan baki har fuskar su, sannan suja cire dankwalinsu gashin sa'ade da Husnah a kunce, Kubrah da bata da yawan gashin kitso ne akanta, sai Rahilah da aka mata kalaba, suka nufi hanyar dakin yan matan nan, yaran ko tsoron su yi gamo ba su yi ba, suka nufi window bayan dakin su. Suka shiga dakin. Iya kansu yana waje, dan tsiya suna zuwa daidai gadon Yarinyar me suna Zainaru, suka tsaya akanta, tare da tattabata. Bude idanu tayi taga mutane da fararren shiga, wani irin zufa ke zubo mata, jikin tana yana rawa. Ke Kubrah ta kama kukan Akuya. "Imeeeeeeeeeee!" Wani tsalle da Zainaru tayi sai gata a can gadon, a kuwa makafin da suke dakin sun yi kukan akuyar, Rahilah ta kama kukan kare "huuuuhuuu huhu" baki daya dakin ya hautsine da ihu, ganin sun firgita sai faduwa sune suna niman hanyar tsira, su ma suka wuce window da gudu suka koma dakin su, domin baki daya hostle din ya dauki ihu, musamman makafin da suke jin kukan kare da Akuya, tare da mage. Su Umma da wasu mata uku suka tashi kusan dalibai dayawa sun tashi a cikin su har da masu barnan aka je kallon abin da ya faru, Rahilah kasa rike dariyar tayi ganin yadda Prefect Zainaru take kerma, tana zabura........ [29/05, 5:42 pm] usmanlauratu71: Barin dakin sukayi, tare da dariyar mugunta kamar zasu kifa, asalin dariyar yaki tsayawa, musamman Rahilah da ta kasa barin dariyar har garin yayi tsit. Washi gari da asuban fari suka fara bin layin wanka, suna ganin ta fito suka cure wuri guda, kamar munafukai suna dariya kasa ƙasa cigaba da dariya, bayan sun shirya suka nufi dinning suka amshi abinci suka ci, sannan suka wuce makarantar. Haka Yaran nan suka gallabi Prefect duk da ana cin Ubansu amma haka bai saka sun daina fitina ba, sai ma kara kai mi da suke yi. Har lokacin visiting ya zagayo, babu Abuturab ga kowa na Sa'ade yazo amma babu shi, sai leke leke tana niman sa babu shi, sai Sadeeq da ya kawo mata kayan provision kamar yadda Abuturab din yake mata. Lokacin da ya kawo ya mika mata, kallon shi tayi tana motsa bakin ta, sannan ta amshi kayan tana kyakyafta idanu alamar hawaye ne zai zubo mata. Rike hannun shi tayi tana kara kallon shi. Dan dukawa yayi yana faɗin. "Yace zai zo ki jira shi" so take ta tambaye shi, ina ya tafi, amma ba halin haka, hawaye ne ya zubo mata. Ta share tana gyad'a kanta, ya labartawa su Zakaria abin da ya faru, sannan sun yi mishi fatan Alkhairi sosai. *** A bangaren Hajiya Daulah zubwa Dr Sharif da dansa idanu, amma tsabar masifar bata iya saukewa akan su ba, sai akan Taufik da Afiyyah, kullum sai sun sha masifa, babu yadda ta iya dasu tunda haka likita ya ce. Har ta hakura haduwarta da Hajiya Nazirah, sai ga magana ya kuma dawowa sabo fil, wanda har maganar ta girma an fara zancen aure. Ko uban bata gayawa ba. Sai dai ta samu Kannen shi biyu kawu Nura da Laminu, suka shiga maganar suma dake munafukai ne bin bayan ta suka yi har sai aka kai sadakin shi da Sophia. Ranar Laraba. Yau ta kama monday, Dr Sharif yana gidan Aunty Fareedah. Shigowa dakin Aunty tayi cikin ladabi ta zauna a bakin gadon sa. Tana kallon shi, kamar bai manyan ta ba domin ya hadu da hutu da kulawa kamar ba shi ya haifi Abdul Hakim ba, "Madam kina kallon kyakyawan saurayi ne kar ka fita mata su kware min ko?" "Tabjam a wannan shekarun naka wacece kwailar ce zata iya da majinarka " ta fada tana dariya, "kuma haka ne, amma me ya kawo ki nasan kina kitchen ne?" Jim tayi tana kallon shi, kafin ta mike tare da ɗaukar links ta fara kokarin daura mishi a hannun rigar ya ce mata."kuma kika yi shiru" "hmm dama akan Abdul ne ashe kun kai sadakin shi?" Kura mata idanu yayi, cike da mamaki amma sai yayi ta maza ya ce mata. "Eh na manta ne ban gaya miki ba, amma mun kai." Ya fadi haka domin bayan son abin da zai tab'a mutuncinsa. Balle yadda matar sa ta rena na shi. "Allah ya sanya alkhairi" ",Amin Ya Allah Nagode sosai, muje ki ba ni abin karyawa." "Tow muje dama kai yake jira" haka suka fito yaba gaba tana baya har wurin zaman su, duk da yayi kokarin hàdiye abin da Hajiya tayi amma ya kasa manta wannan al'amarin. Har ya gama karyawa ya bar gidan. Ba ƙaramin danne bacin sa yayi ba, ya tafi wurin aiki daga nan ya wuce gidan Hajiya. Yana isa ya same ta a falo ita da Abdul ya zauna a kasa, kamar me niman gafara. "Ashe har an kai sadakin Babana?" Ya tambaye ta, ganin yadda tayi maganar so calm, a take jikinta yayi sanyi ta zuba mishi idanu. "Na zata ranka zai ɓaci ne?" Murmushi yayi wanda zaka fahimci kawai na karfin hali ne, "A'a ai da kai da kayan duk mallakar wuya ce, akan me zan yi fushi Allah ya nuna mana lokacin lafiya" "Amin Ya Allah" duk fada da zafin da yazo da shi sai gashi baki ɗaya yayi sanyi, domin yadda yaga Abdul din a gabanta sai yake ganin kamar idan yayi magana laifin kan Abdul zai sauka. Haka yasa gara ya barta tayi yadda take so, domin yasan do kile wata rana zata zo gabbar da dole sai magana. Dole akwai lokaci yanzu ba damar magana, a kyale ta tayi yadda take so, ba wai a hana ta ba tunda ba mamaki tana da nata dalilin da uzurin don haka ya mata uzuri tayi yadda take so, daga haka ya wuce dakin sa yayi abin da zai yi ya fito. Amma a matsayin shi na shugaba a gidan sa, ya dace tayi gaban ta kenan? Duk sai yaji kansa yayi wani irin girma, kawai bai ce kome ba, amma zai ajiye zancen har zuwa lokacin da ya dace ya mata magana. yana gama abin da ya kawo shi ya bar gidan, yana ganin yadda Abdul yake kallon sa. Duk sai ya bashi tausayi. --- Kwara Zuwa yanzu hankalin Badi'atul Noor ya kwanta, asalima kallon kowa take kar bata san me suke yi ba, tana kwance Mama Hajja ta shigo, cikin girmamawa ta ce mata. "Ranki shi dade, Sultan yana son ganin ki" bude idanu tayi tana kallon Mama Hajja. Murmushi tayi sannan ta ce mata. "Ki ce mishi ina barci" shiru tayi tana kallon kasa, duk da idanun ta a rufe, ta ce mata. "Ina sane ki tafi ki gaya mishi ina barci" "amma sultanah" "Ni nace ki gaya mishi ina barci" "shi kenan " ta juya ta fita har bangaren Sultan, duk mutanen gidan suna zaune, ta shiga cikin falon. "Allah ya baka nasara, tana barci " "Ko dai ta ce miki ki gaya mishi tana barci ne" "A'a Sultanate " shiru falon ya dauka, mikewa yayi zai fita Hajiya Mariya ta ce mishi. "Kuma zuwa zaka yi?" Banza yayi da ita. Ya bar falon, bai sake ya bi ta hanyar waje ba, ta hanyar baya ya bi har ɓangaren ta. Tana kwance a falon sama, da sallama ya shiga falon, kasa ƙasa ta amsa, a hankali yaji wani irin nutsuwa ya shige shi. Ga sanyi da dadin da ya cika ko'ina na falon. Ya zuba mata ido, ta zube sosai kamar ba ita ba. A hankali ya ji kamar wani abu yana mintsinin shi, "Badi'atul" bude ido tayi ta zuba mishi. "Me yasa na kira kika saka tayi karya?" " Ba karya tayi ba, nice nace ta gaya maka ina barci laifi ne?" Zama yayi ya kura mata idanu, "but" "kawai bana son magana ne" "but why?" "Kawai bana son magana ne" "akan wani hujja?" Zama tayi sosai tana hamma, ta ce mishi. "Kawai" "tow laifin me na miki? Ban san meye nayi ba, kike min haka na san dai nayi kokarin adalci ne, Yarana kuwa nayi haka ne domin su samu salama bayan nan me kike so nayi miki? Kin haramta min kanki, wannan a ajiye shi a gefe, kin haramta min duk wani abu me muhimmanci don Allah me kike so nayi!" Wani irin kallo ta mishi kafin ta ce mishi. "Yanzu kai ko kunya baka ji ba , kake irin wannan zancen? Hmm ku dai maza baku da kunya wallahi" kura mata idanu yayi, "ok kina son na cigaba da niman hakkina da karfi ne," hannayen ta ta kai baya ta duniya dogare tana kallon shi. "Kuma dake ni yarinya ce sai na zuba maka idanu ka turmusa. Allah ya baka lafiya." "Ciwo nake da kike faɗin Allah ya bani lafiya?" "Kafi kama da me jinya ai, kai baka san ka girma ba ne?" "Eh amma ba shi ya kawo ni ba, nazo magana ne akan me yasa kike disrespect dina?" Kallon shi tayi baki sake. "Kasan me? Idan rigima kake ji ka tafi akwai masu iya taya ka, ni bani da lokacin magana da kai" "kenan kin mai dani mahaukaci kika mai dani?" "An zo wurin " ta fada tana gyara zama, "kamar ya an zo wurin?" Ya kuma tambayarta. "Ai ni lokacin da nake binka ina rokon ka kyale min Yaro bai da lafiya ya shigo ka sauraren Ni? Asalima share ni kayi don haka zaka iya tafiya, kuma ina ganin zancen auren mun tara shi a gefe sai bayan binciken abin da ya faru ya kammala zaka zauna muyi magana irin ta gaskiya. Amma yanzu ni ba matar ka ba ne" "wallahi baki isa ba, baki isa ba nace miki " " na isa wallahi na isa nayi tsaroro, kuma kana ji kana gani idan gaskiya tayi halin halin ta zan buga zawarci me tsada nayi aure ba bar maka gidan ka" kaman wanda ta yarfa mishi wuta haka yaji maganar banbarakwai, "lallai baki da hankali na kuma yarda yau baki da hankali sam baki san me ya dace ki fada ba, ko nace baki da lissafi, me lissafi baya abin da kike yi, aure kuwa yanzu aka fara domin wallahi ba zan tab'a rabuwa da ke ba." Fahimtar maganar rabuwar ya bata mishi rai, ta kuwa shiga maimaitawa aure zata yi har da zawarawa kuma kamar yadda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce tayi idda a ɗakinta haka zata yi, bawan Allah nan ya shiga bala'i kamar zai rufe ta da duka... Tsuntuwa=₦400 Ashraf=₦800 Sanin Gaibu=1000 08130269641 [30/05, 11:21 am] usmanlauratu71: Haka Ummi ta gama zurma shi ya bar sashinta a fusace, kamar zai hada sama da kasa ya tashi, koda ya isa bangaren sa wuce su yayi. Da idanu suka bishi domin sun san ya fita lafiya, gashi ya dawo a fusace, kenan ta bata mishi rai bari ya zo ya sauke kuncin sa a kan sa, wanda haka ya b'atawa Sultanate rai ta mike itama ta fita, don bakar jaraba, ta tsaya iya wurin ta mana, a'a kawai matar nan ta nufi bangaren Sultanah, tun daga bakin kofar take ruwan Bala'i da masifa, sultanah tana fara jin hayaniyar ta, dole ta sauko tana faɗin."Allah ya baki lafiya da nisan kwana an yi miki wani abu ne?" Kamar wacce aka gaya mata magana, ta shiga masifa. "Ki ce na mutu kawai, meye Abdurrhmanu ya miki?" Tab'e baki tayi ta nufi wurin zama tana faɗin. "Babu abin da ya haɗa mu, kawai yana jin rikici ne a ransa" sake baki Sultanate tayi tana faɗin. "Kenan haka kawai yake kunci bayan nan yazo kika dagula mishi lissafi, Badi'atul kiji tsoron Allah fa" wani shan mur Ummi tayi tana fadin. "Ki tambaye shi meye nayi mishi da zai kai kara na wurin? Lallai ma zai zo ya same ni?" Zaro idanu Sultanate tayi tana kara rike sandarta tace mata. "Me zaki mishi? Iyeee me zaki mishi nace?" Shiru tayi bata ce mata uffan ba, domin bata jin tayi iya magana. "Idan ma saboda Yaranki kike haka to ki sani sun tafi kenan gara su zauna a can, ina dalili ke ranki ke kadai kin haifi Yara zama uku, kowa a gidan nan Yaransa maza daya biyu, ke da an kyale ki wasu Mazan zaki haifa bayan matan nan tow wallahi ahir dinki " "Sultanate kenan saboda na haifi Yara maza shi yasa aka watsa min kan su?" Shiru Sultanate tayi tana nazarin katobarar da tayi, a hankali ta ce ."Eh tow, ga zahiri tunda kin saka shi a gaba idan ya mutu fa?" Karewa Sultanate kallo tayi tabbas sakon daga kasar zuciyar ta ne, ba daga saman bakinta yake ba. "Kwanan shi ne ya kare, hmm" domin nade taburman kunyar ta da hauka, ai kuwa ta hau masifa da bala'i, kamar zata daki sultanan, ita dai idanu ya zuba musu har ta gama masifar ta, ta bar gidan. Tana fita ta kira Maina, sun jima suna magana akan Abuturab ya gaya mata har yanzu jikin yaki dad'i, ya ki kuma a kai shi asibiti yana kwane a gida da ciwon. "Idan ka koma ka bashi wayar muyi magana" "in sha Allah Ummin mu" Duk sai taji bata jin wani dadi domin bata san yadda suke bashi kulawa ba, da tana kusa ne zata fi bashi kulawa yadda ya da ce, sama da yadda suke ba shi. Ko ya yake oho? Ta fada a ranta tana tagumi. Kasa hakuri tayi ta kira shukriya matar Maina din tasan tana gida. "Barka Ummin mu!" "Yawwa shukriya, ya jikin Baba karami?" "Alhamdulillahi, Ummin mu yaki zuwa asibiti wallahi" ta fada a dame. "Ok kai mishi wayar yana ina ne ma tukun?" "Yana dakin da, tare da Latifah yar kawu Khamal " "shi kenan kai mishi " kashe wayar tayi, can ta kuma kiran su. "Auta na!" "Ummina!" Ya kira sunan ta. "Ummi mutuwa zan yi?" "In sha Allah ba zaka mutu ba, sai naga Ƴaran ka. Kamar yadda naga na yan uwanka." "Ummina me yasa suka kashe min Babe?" "Kwananta ne ya ƙare? Kayi hakuri sai kace ba namiji ba, kana son ka nuna cewa ba kai Allah bai isa yayi ikon sa bane? Don Allah ka hakura akwai abubuwa da ya dace ka sani ban gaya maka ba, gudun haka gara ka daura damara domin isa inda ya dace. Allah ya muku albarka." "Amin Ya Allah " ya faɗa, daga nan ta daura da nasiha, tare da jan shi da hira. Kamar yadda take son haka yayi ta amsa mata, yana kara tabbatar mata da in sha Allah zai tafi asibitin. Da haka suka yi sallama. Ta zubawa kofar ɗakinta idanu, Sultan ne tsaye kamar ba shi ne ya bar dakin ba minti arba'in da suka wuce ba, ga shi ya kuma dawowa. Mikewa zata yi wuce bakin daki ya riko hannunta. "Me yasa ba zaki tsaya muyi tsayayya magana ba.?" Tab'e baki tayi sannan ta ce mishi. "A gani na, ai mun wuce zancen nan ko? Tow kuwa babu amfanin dawo da shi baya " "amma meye gaskiyar zaki kashe aurenki?" Galala tayi tana kallon shi. "Lallai ma akan wannan ka dawo dama? Hmm" ta wuce bakin daki ta saka key abinta a ranta tana faɗin 'aiki ne bai ishe ka, da ya ishe ka ba zaka zo tambaya ba, Allah na tuba ko mutuwa kayi ai na gama aure balle da ranka, kaji yadda ake ji ne kai ma' ** Birnin London. A hankali ya fito Latifah tana rike da hannunsa, gefen shi Saraki ne. Ya mishi duk abin da zai yi na ganin likita, Na'ima matar Saraki na gefe tana mishi sannu. Kamar su mai da shi cikin su, duk wani zirga-zirga Saraki yayi, koda ya samu ganin likitan bashi gado suka yi aka shi kula da shi kamar me. A hankali sai da ya kwashe kwana biyar, ana kula da shi kafin suka sallame shi, ya dawo gida. Bai yarda da kowa ba, sai matan Yayunsa suma don suna Yayun Mansurah ne, a wannan karon ko Zuwairah kin bata fuskar yayi ya mai sa hankalin shi akan abin da yake gaban sa. Sai dai ya sauya sosai, idan ba a gaban ummin sa ba, ya ajiye wannan shegen shagwab'ar, ya juye ya koma namiji sak. Tun lokacin da yaji labarin mutuwar Mansurah baki daya ko hira haka bayi da lokacin yi da kowa sai ma Ƴaran Yayunsa idan suka ga ya bata shiru zasu biyo shi daki su dame shi da surutu, haka zai zuba musu idanu har su gama. Ya sakawa kansa shirun dole, musamman idan ya tuna yadda mahaifin su ya ki amincewa Ya bar shi ya shiga cikin gidan su, wannan abin yana burning dinsa very crazy, zai yi wuya ka fahimci yadda yaƙe. Tun tasowar sa ake son hada shi da mahaifinsa amma ba a cikin nasarar haka ba, sai akan mutuwar a bar kaunar sa, idan ka kalli fuskar shi kamar bai tab'a dariya ba, ba hmm ba uhmmm. Ai kuwa wani irin yanayi ne mara daɗi ga shiru kamar kurma, kai baki daya Abuturab ya masifar sauyawa wanda hakan ya sa dole yan uwan suka kira mahaifiyar su suka gaya mata halin da ake ciki, a cikin kasa da wata guda. Ya zama sai a hankali, jin haka yasa ta d'aga hankalin ta, domin tsoron kar kunci yasa shi hàdiye zuciyar shi ya mutu, sai da suka kai ruwa rana kafin Sultan ya barta tazo, tare da drive uncle Khamil suka tafi daukota, lokacin da ta iso cikin babban ma shigar, baza idanu tayi tana nimansa, cikin ikon Allah ya d'ago mata hannu. Lokacin da ta ganshi sai da jikinta yayi sanyi, da sauri ya nufe ta. Tare da amso kayanta yana kallon ta. "Abuturab kashe kanka zaka yi ne? " Ta fada tana kara mamakin sa. Wato baki daya tsoro ya bata, bata tab'a zatan al'amarin ya kai har haka ba, sai yau domin duk gaya mata da Maina ko Saraki suke gani take kawai sun kasa fahimtar shi ne, sai yau da ta ganshi da Idanunta. Jikinta yayi sanyi sosai haka suka nufi har gida, idan tayi mishi magana sai dai yayi mata yake, haka suka isa gidan. Shi ya kwashe kayan. Ita can part din Dan uwanta ta sauka anan tayi wanka ta huta can sai ga su Zawairah da Jalilah, Matar Khamal dake irin mutanen nan ne masu wuyar sha'ani, bata yarda da kowa ba sai danginta bata sake da su Zuwairah ba, ganin yadda suke mata sintiri tacewa Ummin su ."Badi'atul nifa mahadimanki wallahi haka kawai ban.yarda da su ba, tsoro suke bani." Dariya Ummi tayi tana faɗin. "Tun rasuwar Khatoon kika kasa yarda da hadimai tow idan Allah yasa ya Khamal zai zama.sarki ya zaki yi hala turawa zaki kwaso mana a gida?" Dariya ta saka ta ce mata. "Ni Kudirat ta ya zan kwaso turawa, kawai jini na ne yaki yarda da duk wani wanda zai fito daga cikin gidan sarautar nan, tun bayan mutuwar Khatoon nake jin a jikina basu da gaskiya duk wanda yake cikin masarautar nan " shigowar Abuturab yasa ta zuba mishi idanu."Son kaga yadda ka tara kasumba kuwa? Don Allah jeka a maka askin ka dawo kai ma ai zaka huta da wannan yanayin." "Yes Ma " ha fada yana barin falon. "Kudirat haka ya koma?" "Eh baki gani ba, kaf idan ya akwai wanda yake kulawa tow na miki karya domin duk nace na Mimi haka ta bar sa, baya magana daga Yes sai Ok, iya su ke hada shi da yan uwansa, don ko shekaranjiya sai da Daddy ya mishi fada, na dai ji suna cewa zai koma makaranta, idan ya shiga cikin jama'a dai dan samu karfin fada da kansa domin kuwa a halin yanzu ya kasa fada da kansa ne, zuciyar shi taci karfin shi ne da zai iya yaki da ita tow da wasu abubuwan zasu yi sauki. "Gani nake kamar ba Abuturab dina ba, ya sauya sosai." "Ki cigaba da addu'a domin shi yake bukata wannan shirun na shi, ai ba kanta" inji Hajiya Kudirat, "haka ne kan zan kara kaimi kafin na koma zamu tafi Saudiya da shi ko zai samu sauki wasu abubuwan in sha Allah." Abinci taci kaɗan, can kuwa sai gashi ya kuma shigowa fuskar tayi kyau. Zama yayi ta zubo mishi abinci. "Ummi i'm ok" watsa mishi harara tayi. "Oya bude baƙi, ba dole ka lalace ba, babu walwla babu cin abinci mutum ya kare kamar kudin guzuri." Ta shiga bashi abinci yana ci, tana rarrashinsa. Shigowa Latifah tayi ta same su a haka, sai ta ji sun masifar burgeta, ta zauna me bude bakinta itama ana saka mata abincin. Duk da yamma tayi sai da Ummi ta saka su a gaba suka fita. Abubuwan da suke damun sa, har da nauyin Sa'ade da bai sauke ba, gani yake bai kyauta ba, da bai nime ta ba bai gaya mata gaskiya waye shi ba, ga Mansurah ta tafi ta bar shi, yanzu yasan tazarar da take tsakanin su. Ba zai bata damar ganin shi ba, na cewa zai dawo. A hankali ya fara sake jikinsa domin ummi, amma ba dan kansa ba. Duk da haka sai da Ummi ta shirya mishi ganin likita na musamman. Ta kai shi. Likitan ya dube shi bayan sun gaisa da junan su. Sannan ya ce mishi. "Mr Ali. Meke damun ka?" Shiru yayi yana kallon window kasancewar su suna lokacin zafi ne . "Mr Ali ina jinka?" Kallon Likitan yayi sannan ya ce mishi. "Babu kome!" "Babu kome gashi Mahaifiyar ka ce ta kawo ka." "Eh babu kome Dr" "ka tab'a shiga mugun yanayi ne a rayuwar ka? Ko ka tab'a jin babu dad'i a wani abu da ya faru da kai?" Murmushi yake yayi sannan ya ce mishi. "Babu bana jin dadin rayuwa ne kawai" "kamar ya?" Shiru yayi yana cup na coffee da aka ba shi. "Tun ina yaro na taso tare da ita ne, ban tab'a barin wani abu ya cutar da ita ba, sai da aka mana baiko ta rasu, shi ne nake jin babu dad'i " kallon shi Dr din yayi. "Kenan mutuwar ta shi ya saka ka shiga kunci da damuwa?" "Eh tow bana ce ba, amma kuma ina kewar ta." "Amma addinin musulunci ya baku wasu abubuwan da matukar naku ya mutu kuna mishi ai, ko kai baka yi ne?" D'ago kai yayi yana kallon likitan, sannan ya yi murmushin dole ya ce. "Dole ne wannan." "Tow me yasa ba ka manta da ita ka nime auren wata ba?" Kurban shayi yayi sannan ya ce. "Niman auren wata ba sauki, domin sai ka fara jin qarfin yin soyayya kafin har akai da zancen aure, kaga kenan duk yadda zaka yi dole sai an dauki wani mataki na rayuwa kafin a cimma wani mafita " ........ Yau kan na sallame ku, idan kuka min comments na kuma yin wani da yamma idan babu ku huta na huta.🤣🙄🚶 08130269641 [31/05, 9:04 am] usmanlauratu71: "Amma ai da ka jarabawa, idan baka manta ba, akwai mutanen da suke dakon jiran haka a tare da kai, cikin su har da Mahaifayar ka, ko kafi son ganin ta cikin kunci da damuwa ne?" Murmushi yayi yana kallon ruwan coffee ɗin ya ce. "Ba ni da burin saka su damuwa, sai dai zuciyata tayi nisan da ba zata ji kira ba, idan lokaci yayi kome zai sauya. Kome zai koma muhallin sa na ainihi, amma yanzu bani da karsashin da zan iya tunkarar mace domin nasan daga ni har ita wahalar da kan mu zamu yi toh me zai saka mu bawa juna wahala." Shiru likitan yayi kafin ya ce mishi. "Bayan yarinyar da ka rasu ka taba haduwa da mace?" Shiru yayi kafin ya girgiza kai, "Ban hadu da wata mace ba, sai wata yarinya karama da na tsaya muka kai ta makarantar nakasassu." Kallon shi likitan yayi. "Yarinya kuma? Zata kai shekaru nawa?" Ajiye kofin yayi yana faɗin. "Ka gama ko akwai saura?" Yadda ya mike sai ya bawa Likitan dariya, yayi murmushi sannan ya mika mishi hannu suka kara musabaha suka fito, suna kara tattaunawa, sannan likitan ya kalle shi na wani lokaci kafin ya ce. "Baka da matsalar kome, matukar ba bad nightmares kake ba, sannan damuwar ka bata da yawan da zata hana barci, kewar ta ne bai fita a ranka ba. Amma yana da kyau kana dan fita shan iska, kamar kallon kwallon, yan tafiye-tafiye yawon buɗe ido, ko zuwa bakin beach, idan ta kama shiga kungiyoyin agaji da taimako yana da kyau domin zai rage maka damuwar ka, zaka ga kamar kai ba damuwar ce da kai ba, akwai wad'ada nasu tafi naka, ka kula sosai idan kasamu hali ka kara tuntubana." "Ok " ya fada bayan ya fito, Ummi da Latifah ne zaune suna jiransa. "Ka fito auta?" "Eh ummina " "Ummin mu dai ko Ummi?" Murmushi tayi, sannan ta wuce wurin likitan, suka wuce cikin office din shi. "Sannu Ma, Ali bai da matsalar ko me, sai ta kewar yarinyar da ta rasu, sannan a hiran da muka yi da shi, akwai wata Yarinyar da ya hadu da ita, ina ga ba mamaki idan da zai zauna kusa da ita tow walwalar shi zata dawo sosai" "wacece ita haka? Kuma me yasa ka fadi haka?" Gyara zama likitan yayi, sannan ya a labarta mata yadda suka yi da Abuturab, shiru tayi, kafin ta ce mishi. "Yanzu babu maganin da za a daura shi a kai?" "Babu, shi da kansa zai bawa kansa magani, domin yakin ba na kowa ba ne na kansa ne, shi da kasan zai yaki kansa matukar ana son ya dawo daidai sai ya tsaya tsayin daka ya bawa kansa kome, babu wanda ya isa mishi wannan fadar kin fahimta, ko wacce yarinyar da ya sako a zancen shi ba wai ya sako don yana da wani abu da ita ba ne, asalima kamar yana jin babu dad'i ya tafi ya bar ta, ba tare da ya ce mata good bye ba. Amma idan ya kasance haka ne zai iya nimanta har ya mata sallama." "Na gode sosai likita, bayan bayan nan babu wani abu?" "Eh tow na gaya mishi abubuwan da ya dace yayi domin samun sauƙin shi." Anan ya zayyano mata abubuwan da ya dace su. Tayi mishi godiya suka bar asibitin, tun daga lokacin Ummi ta lashi takobin ba zata bar shi ba, sai ta saka shi ya daina kuncin nan. Kuma haka ne, haka suka ta cigaba da tafiya da shi, haka ta dauke shi su je nan, su je can. Idan ta kama kallon kwallo ne a tare suke tafiya, a cikin wannan yanayin suka tafi umra, babu laifi ya sake sosai, sai dai rashin magana ne kamar ba shi ba, duk da yadda Latifa take makale mishi, kuma itama Ummi ta yaba da halin ta, yasa duk inda zasu tana me janyo hankalin yarinyar, tana dakyau ga hankali uwa Uba bata da hayaniya kamar na sauran yan matan, kuma sai ta ga dacewar su da shi Abuturab din domin yarinyar bata da fitina da kiriniya. Haka suka cigaba da mishi addu'a da kulawar da suke ba shi ba na wasa bane, haka yasa shi dole yake sakewa ko dan Umminsu. A can gida Nigeria kuwa, tun Sultan yana dauke kai idan aka mishi maganar abin da Sultanah Badi'atul Noor tayi har ya kasa hakuri, domin dai tunda ta bar musu gidan tace kowa ya ci kansa, yake cikin damuwa, duk abin da za ayi baya burge shi, asalima yayi ta fada kenan, sun rena shi sun biyewa Badi'atul Noor suna mishi abin da ransu yaso, don haka kar ya ga kafar kowa a bangaren shi, yau kusan sati hudu ake nima da tafiyar ta, yana zaune shi kadai a dakinsa. Ya bude idanun ya zubawa wani karamin hoton ta idanu da yake gefen gadonsa idanu. Hoton tayi shi tun da kuruciyar ta ne, don haka ya saka shi a wannan wurin domin dakin bai zama a cikin sa, kuma ba a cikin yake kwana da matan shi ba. Yana son Badi'atul Noor matsalar ta cika rashin kunya ne, kuma tun can baya haka take, wayar shi ya janyo sha biyu saura, kiran layinta tayi a kashe don Allah ya kira Layin Maina ya same shi. "Assalamu alaikum, Barka da dare Abba" "wa'alaikumunsalam Barka dai, amma kunyi hankali da kuka rike min mata ta? Akwai adalci a cikin wannan al'amarin? Fisabilillah idan bata yi tunanin dawowa ba, ku ba zaku tuna mata zaman aure take ba, sai ta zauna a tsakanin ku tana kalle muku mata idan ba a muku daidai ba, ta hau masifa an mallake mata Yara?" Yadda yake fada zaka rantse da Allah wani abu aka mishi, yana gama fadar Maina ya bashi hakuri, yana tari. "Mura ya kama ka baka je asibiti ba?" "Eh amma zanje in sha Allah, bai wani jima da kama ni ba " da haka sukayi sallama, washi gari da safe, Maina ya da ya shiga cikin gidan Kawunsu ya ce mata. "Ummina yaushe zaki koma gida ne?" Kallon shi tayi kafin ta haɗe rai ta ce. "Abban ku ya kira ka ne?" Shiga nutsuwar shi yayi sannan ya ce mata. "Eh ki kira shi" nan ma ya fara tarin, "yaushe mura ya kamaka, naga zafi ake yi?" "Eh zan je asibiti na ga likita" "Allah ya baka lafiya" "Amin Ya Allah, zan tafi wurin aiki" "Allah ya bada abin da aka je nima, ya kuma bada sa'a" "Allahumma Amin." Haka ya bar gidan yana girmama rigimar da za ayi tsakanin iyayen su, bayan fitar shi ta kira Layin Sultan. Dauka yayi cikin niman rigima ya fara sauke mata halin uwar shi, sai da ya gama jidalin shi , ta ce mishi. "Kasan Allah ka kuma sako min Yarana cikin maganar mu sai dai wata ba ni ba, ka tab'a jin labarin mace ta sake namiji? Tow a kaina za a fara, wallahi ka fita Idanuna na rufe ba zan dawo ba, da kake cewa matan Yarana zan saka musu ido waye ya gaya maka ina da wannan halin, babu abin da ya dame ni da su, idan matan su, sun so su dafa su babu abin da ya dame ni. Kai da kake da mata me zaka yi da akwala irina. Aure kuma idan nace bana yi babu me min dole ka fahimta?" "Amma Badi'atul Noor fisabilillahi tun tuni baki yi yaji ko fushi ba, sai yanzu da jikoki suka miki kawanya? Na zata idan nayi kuskure zaki zauna dani a haka ne, don Allah ki dawo dakin ki ina bukatar ganin ki a haka, bana jin dadin rayuwata." Baki daya yadda yake kalaman in romantic da rarrashi yasa jikinta yayi sanyi ya ce mata. "idan ma ni kike son gani nazo daukar ki, in sha Allah jibi ina hanyar zuwa, don Allah kar ki ce min a'a, kin ji Nur" shiru tayi kamar zata ce mishi ba sai ya zo ba, amma ta nunawa uwar shi da Matan shi ita fa mijin su ya dama, shi yasa suke bin shi, ita kuma Sultanate danta babu yadda zata yi da shi Allah ya kulla sai tayi hakuri. "Ok kazo ka ɗauke ni" "da gaske?" Ya tambaye ta? "Eh da gaske mana, na tab'a maka wasa ne?" "In Sha Allah zaki ganni." Ya fada cikin zumudi, ai dama ba cewa tayi bata son shi ba, rashin fahimta ce kawai da kuma shiga makiya a tsakanin su yake haifar musu da rashin zaman lafiya, da za a tsaga jikinta jinin shi yake yawo lungu da sakon jikinsa, bata jin zata yi butulci akan zaman su, tunda kome ka gani mukaddari ne, daga rabbil alamina, sannan zata iya daukar haka a matsayin kaddaran ta ce, babu wani abu da zata iya sauyawa akan rayuwar ta ko na Yaranta, shi yasa take kara zage damtse sosai wurin tsayawa Yaranta da shi kansa Sultan din. Koda Sultan din ya bayyana tafiyar shi London, abin bawa Kowa mamaki duba da yadda Badi'atul Noor tayi tafiyar dutse a hannun riga yasa baki daya haushi ya kama Mariya da Badariyyah uwa Uba Turai ai gani suke su da basu kai ta girma ba, baya wannan azarbabbin balle ita da ta girma, wani irin munafikin jiki ne da ita wallahi baya nuna girman ta, kai ko irin tumbin nan bata da shi balle har ka ga alamar girmanta, a iya gashin kanta ne zaka fahimci haka da muryanta amma bayan haka gyara jikinta take ba Bala'in, bata wasa da gyaran jiki hatta cimarta ba irin tasu bane, ba kome take zubawa cikin ta ba, wani abin da basu sani ba, har abin motsa jiki tana da shi a ɓangarenta, su kuwa kowa ka gan shi ya zama rusheshe. Kuma su masu aiki ke kula da cikin su, ita kuwa taki yarda da haka. Ita ke sarrafa kome nata shi yasa take kara haukata Sultan babu abin da ya dame ta. Haka suka gama ihun su, itama Sultanate ta gama mitar ta, ta hakura tunda bata da yadda ta iya, sai dai tana kan bakanta har abada Yaran Badi'atul Noor ba zasu tab'a zama cikin masarautar ba, domin ta lura baki daya so suke su raba danta da muka mishi sa, ita ba zata ma iya daukar wannan ganganci ba, zata ci mutuncin su daga Sultan din har Badi'atul Noor tunda ta lura yarinyar bata da mutunci so take kimar shi ta b'are. Zata yi maganin ta. *** Wannan karon visiting din ya zo babu dad'i, duk kiriniyar Sa'ade daga ranar tazo zata koma wani kalar tausayi, ga Sadeeq shima an dauke shi a Sokoto, ya koma gombe duk sai ta koma kamar mareniya. Babu Abuturab babu Sadeeq, kallon yan uwanta maza da mata tayi, tana son tambayar su Inna amma bata san yadda zata fahimta ba, riko hannun Yusuf tayi tana kai hannunta goshi, "me yasa innar mu bata zo ba?" ........ "Muna cikin rashin wuta ayi maneji" Top-notch 08130269641 [01/06, 4:36 pm] usmanlauratu71: 30807 A haka harsu ya faru a lokacin domin Rahilah kuka tayi ta musu ba zata tafi gida ba, da a zava barta tow da ta zauna a makarantar, amma babu hali. Duk da sauran na murnan komawa gida amma ban da ita, ganin yadda take takure ne yasa Sa'ade itama shiga cikin damuwa, domin ko da ta tambaye ta meke damunta. Cewa tayi babu kome, har suka gama jarabawa, baka gane kanta. Kwanakin da suka biyo baya kawai, suna tare ne amma babu dad'i. Kamar an musu mutuwa, ranar da zasu yi hutu kuwa kwana suka yi suna hira. Washi gari suna cancad'a kwalliya aka zo aka ɗauki kowa, Sa'ade da Rahilah karshe, shi yasa da aka zo daukar ta, taki tana son ta ga tafiyar Rahilah. Haka kuwa ya faru, wurin karfe biyu na rana aka zo daukar ta, suna rike da hannun juna, haka suka yi ta kuka. Dakyar aka raba su. Sannan suka tafi cike da kewar junan su... *** Abdul Hakim. Biki budiri bured'ed'e,, anyi bikin da ba a tab'a yi ba, domin Ƴaran iyayen su manyan ne masu kumbar susa. Anyi wasa da dukiya kamar ba a aso. Anyi barna da almubazzaranci, sai dai muyi fatan Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a dayyiba. A bangaren ango kuwa babu abin da saka ce ya karu da shi a auren sai ciwon kai da kuma barazanar da ciwon shi yake kan yi na alamar zai tashi. Haka ya wuce gidan shi da yake bayan gidan Hajiyar shi. Anan suka tare, kullum Afiyyah da Taufiq suna gidan. Tun bikin da Aunty Faridah tazo, taga irin matar da aka aura mishi sam yarinyar bata mata ba, domin tana da Bala'in reni da rawan kai don ko da aka ce mata ga matar Babansa ta zo, wani kallon shekeke ta mata, haka yasa baki ɗaya take tausayin rayuwar Abdul din irin matar da uwar shi take so kenan, bayan biki da kwanaki ya kaita gidan Aunty Fareedah, ba laifi ta samu tarba na musamman, har kunya sai da ya kama yarinyar nan domin yadda ake mutunta kuwa. Daga nan gidan Iyayenta ya kaita. Har zuwa lokacin babu wani abu da zata ce na aure ya shiga tsakanin su, sai ma ƙara lalacewa hakan domin tsakanin su ina kwana, baya iya kome asalima baya dawowa gidan akan lokaci koda ya dawo ba zai shiga ba. Haka ya faru ne sakamakon shigar da take yi a gidan, idan ya ce zai dauka tow zai iya mutuwa, a cikin kwanakin akwai abin al'ajabi da ya faru, ya fito wanka ta shigo dakin. Duk da ya so kauce Mata. Amma dake yarinyar wayo da ita, haka ta saka shi a gaba bai san yadda aka yi ya biye mata ba. Sai da yaji kamar ana zare numfashin da daga jikin shi, saboda yana kokarin motsa jikin sa ya sarrafa amma abin yaci tura ƙarshe suma yayi a wurin, faruwar haka yasa ta nufar gidan Hajiya ta gaya mata suka fito aka kai shi asibitin, dalilin wannan yanayin yasa dole Hajiya ta dawo da Sophia gidan ta, don a yadda likita ya mata bayani danta matukar aka ce sai wani abu ya faru a tsakanin su tow zai mutu. Gani take kamar karya ne anyi haka ne domin a rufe ta. Shi yasa tun da Abdul ya farka ta haushi da masifa da bala'i kamar zata rufe shi da duka. Inda take shiga, ba nan take fita ba abin tausayi, sunkuyar da kai yayi yana rike da Kirjinsa. Har ta gama Bala'i bai ce mata cikanki ba, a haka ya samu awa uku, ta matsa lallai a sallame sa. Haka aka suka sallame shi, suka nufi gidan Hajiya. *** Maikulki. An samu cigaba yadda ba a zato ba tsammani, domin ta ko ina ka shiga zaka samu mutane suna kokarin fitar da yaran su zuwa makarantu har cikin sunkuru, makiyaya da manoma suna kokarin fito da yaran su niman ilimin zamani da na addini, sau tari mutane zaka samu suna yiwa Malam Aminu ba'a da cewa, yar da aka nime kaita bara yau ita ce tayi mana sanadin da yaran mu suke samun karatu da ilimi, tun abin baya damu n shi har ya kai ya fara damunsa, ya daina fita waje ko sallah ma a cikin gidan shi yake, a hankali abin da ya shika ya fara girban sa, domin yadda ya tsangwame Sa'ade sai gashi shima da girmansa mutane sun tsangwame shi har da mishi habaici da bakaken magana ake cisga mishi wanda yasa shi shiga kunci da damuwa, yana ji yana gani depression ya sako shi a gaba. Yau juma'a yana son ya fita sallar juma'a amma tsoron abin da zai iya faruwa yasa shi ƙwanciyar shi a dakin shi. Yana tunanin yadda yayiwa Sa'ade shima yau gashi duniya ta mishi daurin goro. D'aga labulen dakin sa Inna tayi tana kallon shi, yadda ya koma yasa ta shiga dakin tana faɗin. "Yanzu yau juma'a rana me falala da albarka malam kana kwance a dakin ka? Wai na tambaye ka Malam meke faruwa ne?" "Babu kome, hmm" ya fada yana kallon kofar dakin. "Ya zaka ce babu kome bayan gashi nan ana iya hango damuwa karara bisa fuskar ka. Meke faruwa ne?" "Ina yaron nan Aliyu da yake zuwa?" Ya tambaye ta kansa a sunkuye. "Ina jinka" "hmmm dama na sayar masa da Sa...." Kura mishi idanu tayi tana kallon sa. "Ka sayar mishi da Sa'ade ba? Ai na jima da sanin haka, Allah ya kyau yanzu yasa ka shiga damuwa?" "Hmmm ban san inda yake ba, na nime shi na bashi kudin sa ne ya dawo min da ita ban gan shi ba, karshe ma Mai gari ya tabbatar min ya bar garin nan, ina tsoron kar sanadin abin da na aikata rayuwar ta ya lalace " "Allah ya kyauta tunda ka sayar mishi da ita ai kasan ya saye ta, Allah na tuba ko bawa an daina sayar da su, balle yarinyar da Allah ta jarabce ta, da lalura irin na Sa'ade. Ina imanin ka da tausayi suke da zaka sayar da yarinyar da ko magana bata yi, Allah sarki Ubangiji kenan ya kyauta " daga haka ta juya ta koma wurin girkinta har abada ba zata tab'a gaya mishi inda Sa'ade take ba, balle har yayi wani kazamin tunani akanta ba, Allah ya tsare mata Sa'aden ta domin ko wancan satin da Iro yazo ya tabbatar mata da sun yi hutu, shi yasa take hada mata kayan komawa kafin lokacin yayi. Don ma Allah ya bata yara masu tausayi da jin kan junan su, Allah shi ya bata su kuma sai ya sanya mata su a matsayin sanyin idaniyarta, musamman Mazan da Allah ya fifita su ya musu albarka a cikin niman su da sana'ar, matan ma suna kokarin turo mata abubuwan da suka samu, sai dai samun da namiji da na ya mace akwai banbanci. Amma tabbas duk abin da suka samu suna kokarin kaiwa mahaifiyar su. Yanzu Babban abin da yake d'agawa Malam Aminu hankali yadda ake kara cewa ana ganin Abuturab ba dan Najeriya bane, wani abu ya kawo shi kuma ya gama ya koma kasar su, wannan abin ya saka Malam Aminu a cikin tashin hankali da damuwa, domin har ga Allah ciwon tsatsaye yake, ga yawan zurfaffa tunani, wanda haka yasa shi zubewa duk da daman can ba kibar ce da shi ba. *** Kamar yadda Sultan ya yi alkawarin ai kuwa hakan ce ta faru, karfe goma na daren juma'a ya sauka a garin london. Maina da Saraki, suka je tarbo shi. Idan ja ganshi yau babu manyan kaya, shiga ce irin ta zamani. Hannun shi daya riƙe da sandar dogarawa, ba wai dogarawa ta lalura ba. A'a ita kanta rike sanda a hannu sunnar annbawan Allah, kuma basaske don haka kusan kwalliyar sarakai ne rike sanda a hannun su, haka yasa shi fitowa dass da shi. Loggers din shi Maina ya amsa. Yana murmushi domin sun bar Ummi ana mata henna, jiya zuwa yayi aka mata gyaran gashi, shi ne ma ya ajiye ta a wurin saloon din, yana jin Shukriya matar shi tana cewa no wonder mai Sultan yake fadar sun rike mishi mata, kawai tsabar kulawa ce da lafiyar jiki da kuma abincin sa. Domin kafin a fara mata lallen sai ta ta gama daura kome sauran su Shukriya zasu karasa. "Ina baba karami?" Kallon juna suka yi da Saraki, kafin suka san yadda zasu kare dan autan su. "Ya tafi makaranta" "wani irin makaranta yaushe ya fara?" Tarin da Maina ya fara yasa suka zuba mishi idanu. Tari har da rike kirjin shi. "Ka je asibiti kuwa?" Gyada kai yayi yana sauke numfashi, fita yayi da sauri ya samu irin babu mutane ya zubda bakin majina me had'e da jini. "Maina anya kaje asibitin ban yarda da kai ba ne wallahi" "wallahi na je har hoton kirjin aka min amma babu kome sun ce ina shan ruwan sanyi ne!" Cikin b'acin rai Sultan ya kalle shi ya ce mishi."hala kai yaro ne da za ace kar ka sha ruwan sanyi, ka kula da lafiyar ja da rayuwar ka, yau ko babu mutuwa akwai tsufa dole idan ma gaji da mulkin nan kai zan bawa ko Saraki?" "Haka ne Abba " ya kalli Maina yana dariya. Girgiza kai Maina yayi ya zauna a gefen shi Direba Saraki yana jan motar, "Abba mulkin kwara ta me zafin nama ne da sanin halin mutanen cikin sa, Allah ya gani bana sha'awar mulki sai dai ko Saraki" wani wawan burki saraki ya taka. "Kasan me ka fada?" " Na sani mana, ni fa jikina yana bani, cewa rayuwata ba ta da tsawo." Gaban Sultan ne ya fadi. Kallon Maina saraki yayi ya ce mishi. "Like me nima ina jin kamar bani da sauran tsawon shekaru da rayuwa." "Dan kun ganni ne kuke gaya min zaku mutu ku bar ni?" "Afwa Abba"suka fada kusan dukkan su lokaci guda. Haka suka isa gidan jikin su a sanyayye. Har ɓangaren baki suka kai Abban su, an gyara wurin tass. Maina ya wuce cikin gidan, daurewa yake daman yana shiga dakin sa ya saka key, ya cire rigar shi Wasu irin rashes ne a gefen hakarkarinsa, sunyi jajjur. Haka ya shiga ban dakin yayi ta kwara ruwa, yana gamawa tari ya ce gani, ashe dama bai yi ba da sai yanzu tari har da jini ta hanci ta baki. Sai da yayi sosai fuskar shi tayi wani irin fayau, kamar babu jini a jikin shi. Yana gamawa ya wanke fuskar shi da ruwan zafi, ta yi ja domin idan ba hakan ba zai d'agawa iyayen shi hankali. Shi kuma baya son ya d'aga musu hankali, kusan asibitoccin da suke garin nan babu inda bai je ba, an rasa gane ciwonsa. Har gwanjin Cancer sai da aka mishi amma babu wani Cancer ciwo ne dai kawai. ALLAH YA MANA MAGANIN CIWON DA BAMU SANI BA... [02/06, 6:46 pm] usmanlauratu71: Ciwo ne da ba asan kanshi ba, shi yasa shima ya boyewa iyayen shi, wannan al'amarin babu wanda ya sani shi daya yake ta yawo da shi, bayan ya fito ya huta kafin ya nufi part din baki. A can suka hadu baki daya aka bude shafin hira ban da Abuturab da yayi b'atar dabo. Hira sosai aka yi sai magarib aka watse maza suka nufi masallaci, mata kuma suka wuce bangaren su. Sai wajen goma saura Abuturab ya shigo gidan, suna zaune a falo ana hira, ya shiga ya gaida kowa sannan ya kalli Ummi hankalin shi yana kan agogon hannun shi."sai da safen ku, Ummi ki min addu'a gobe muna da interview." Daga haka ya bar falon yana i mamakin ina Abban su. Bai wani damu ba domin ya b'ace ne a gidan don baya son wani abu ya haɗa su, don har yau yana jin zafin Abban su. Hango inuwar mutum yayi kamar mara gaskiya, shan jinin jikinsa yayi akwai wani abu da yake faruwa. Bin inuwa yayi kicibis suka yi da Zuwairah. Kallonta yayi sosai sannan ya ce mata. "Me kike yi a wurin?" "Hmm dama dama, kukan mage na ji nace bari na duba" juyawa yayi bai ce mata kalla ba, bayan tambayar da ya mata. Wucewa dakin shi yayi ya tura zai shiga, yaji motsi a dakin dan dakatawa yayi kafin yayi kasadar shiga, Sultan ya samu a cikin dakin yana duba wasu abubuwan Abuturab din, "Ubana nayi laifi shi ne aka ko zuwa dauko ni?" Yar murmushin yaƙe yayi ya ce."A'a ina niman karamin aiki ne na fita saboda zan koma makaranta." Juyawa yayi sosai ya zuba mishi idanu, baki daya ya sauya daga Aliyu da ya sani. Sai karkad'a key yake. "Na dame ka ko?" "A'a Abba" yasan waye Abuturab, a fusace yake kuma abin da ya dakatar da shi, don shi ne ya haife shi da ace wani ne ya mishi haka, zai ga danyen kai. Nad'e hannu yayi a kirji yace masa. "Kana jin zafina ko?" Dauke kai yayi yana girgizawa. "Tow me yasa?" "Abba na gaya maka gaskiya na tafi." "Abuturab kenan ai nasan halin ka, akwai lokacin da zaka fahimci abinda yasa nayi haka, kai da Mahaifiyar ku, kuna min kallon mara adalci ba? Hmm ka kula da y'an uwanka Maina yana fama da tari, don Allah ka saka idanu akan sa, gobe zamu wuce Nijar daga can zamu wuce gida ne" "Allah ya tsare hanya" takowa yayi a hankali yana kallon yadda kome yake zaune a muhallin sa. "Allah ya muku albarka." "Amin Ya Allah " ya fada a sanyayye, fita Sultan din yayi Abuturab ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya, sai ya ji ya shaƙi iskar yanci. Haka kuwa ya faru da safe suka bar kasar, cike da farin ciki. *** Hutu ya kare, kowani dalibi yana kallon ranar komawa makaranta a matsayin ranar fara damuwa, a gefen Rahilah wani irin farin ciki take cike da shi, ga magana da farin ciki amma ta rasa inda zata fadi haka. Da sassafe Aunty tayi sammako daga gidan ta, ta same ta a dakin su zaune kamar mayya. "Kin gaji ko? Kina son ki koma makarantar ko?" Ta tambaye ta, dake tayi koyarwa a makarantar kafin ta bar aikin ta fara wani. Girgiza kai tayi tana sunkuyar da kai kasa. Tab'a ta tayi tana ce mata. "Taso muje" ta riko jakan Ghana most go dinta, tana kallon yadda yarinyar ta sukurkuce, Mahaifiyar Aunty ce ta fito tana rike baki. "Yanzu sai ki tafi bamu gaisa ba, Auntyn su." "Mama sauri nake zan mai da ita makaranta ne, kuma zamu makara". "ai shi kenan sai ki ta tafi tunda bamu isa ki shigo wurin mu ba" a gaggauce ta shiga dakin Mahaifiyar ta, tasan halin ta sarai, "fisabilillahi tun yaushe nake kiran wayar ki baki dauka ba, amma dake aikin wahala ne kin taso zaki daurawa kanki, bayan Baban ku ma cewa yayi aurar da ita zai yi ya huta" gyara zama tayi sannan ta ce mata. "Mama lokacin Baffa yake raye shi ya rike hannuna har na kai matakin da nake, na rantse da Allah, ba zan iya barci yar shi tana cikin kuncin rayuwa ba, shi yasa na kaita makarantar irin su tunda na lura Baffan mu bata ita min yake ba. Ni dai ina baku shawara kar ku dauka babu rayuwa bayan mutuwa ne akwai domin kuwa Allah yana sane. Kuma ya ji." "Tashi ko ki kaita, Kafin ji fara mana wa"azi alaramiya, sai ku tafi ai" Mamanta ta fada tana aikawa Rahilah harara. Ita dai sunkuyar da kai tayi suka fita da daga gidan. "Kiyi hakuri zaki ji dadin haka wata rana," gyada kai tayi tana mata alamar godiya. Haka suka bar gidan. Tare da nuna mata ledar bagco da ta sako mata kayan abinci da su sabulu, tayi kokari ba laifi don ma sun sake mata nauyin Rahilahn ne ai da ba haka ba, "Allah ya jikan mahaifan ki" domin ba haka suka yi mata ba, yau gashi yar su tana watangaririya. Suna shiga cikin makarantar ana kawo Husnah, ai nan suka kacame da murna, bayan an gama musu kome suka wuce hostle, awa biyu da dawowan su, sai ga Sa'ade. Anan aka bude sabon shafi na farincikin. Washi gari aka kawo Kubrah, suna ganinta aka fara halin niman magana kamar yaran bera. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya da yan matan nan, yau fari gobe tsumma. Ga kokari sai dai a bangaren Sa'ade bata fasa zuba idanun ganin yaushe zai zo ba, tun kawayen basu fahimci akwai abin da yake damunta har suka fara gano ta, idan aka ce yau ranar visiting ne zaka ganta tana kallon bakin get ko zata ganshi. *** Abdul Hakim. A bangaren shi da mahaifiyar sa, ba a cewa kome, hatta Sophia ta fahimci bai da wani kuzari, haka ya janyo wani irin wawan gibbi a tsakanin su, domin reni take da shi. Duk abin da ya mata shi take yi, idan a gidan su ne, a gaban Hajiyar shi kuwa kamar ta cinye shi danye. Duk da yana kokarin boye damuwar shi haka ya janyo mishi ciwon sa ya fara kokarin tashi a kai akai don ma yana Bala'in tsoron Hajiya domin cewa take karya ne ba ciwo bane gulma ce an saka shi ya mata renon hankali ne. Ganin yadda yake kara samun koma baya a kan lafiyar shi, babu shiri Mahaifin shi ya nima mishi mafita, ta hanyar tura shi karatu PhD domin tausayin d'an na shi yaƙe, yasan idan baya nan zata kyale shi, bata san da tafiyar ba sai bayan tafiyar shi Dr Sharif ya gaya mata, domin nan ya bar mata Sophia. *** Kwara. Tunda Badi'atul Noor da Sultan suka dawo, aka gansu tare hankalin sauran matan ya tashi babu kamar Badariyyah, domin ta iya munafinci, amma a ruwan sanyi. Haka tayi ta bin sa akan ya shirya musu tafiya Umra, ya share kamar bai san tana yi ba. Yau girkin Badi'atul Noor ne, duk da taki yarda da zancen haka amma yadda ya kafa ya tsare yasa ta amsar girkin babu yadda ta iya, kuma ta ce mishi ba zata zo ba, tunda ita ba yarinya ba ce. Ya ce ya ji ya gani shi zai je. Akan haka sai da Baffanta Junaidu ya shigo cikin lamarin domin rigima aka tadda shi, matan shi da goyon bayan Sultanate, ita kuwa ta ce bata iya ji ba. Ganin zasu ja mishi salalalar tsiya ya ce musu. " Na amince ni zan na zuwa bangaren ta, su kuma duk wacce ba zata zo ba, tayi zaman ta." Wannan abin ya bakanta ran Sultanate. Don haka babu shiri kowacce ta ce ta amince shi kenan. Shi yasa ake zauna lafiya, shi kansa lallaba Badi'atul Noor yake kamar yana jin Bala'in tsoron ta. Tun sallah isha ya wuce bangaren ta, suna falon sama suna hira kafin su kwanta. Kwankwasa kofar falon aka yi Mama Hajja ce. "Shigo Mama Hajja" ta bada izinin ta shigo. Cikin ladabi ta shigo ya ce mata. "Sultanah Hajiya Badariyyah tana son ganin Sultan" " ta shigo" ta fada tana gyara zaman dan kwalinta. "Tow" ta juya ta fita can sai gata ta shigo bayan cancad'a kwalliyar da tayi. "Barka da Hutawa Sultanah" "Yawwa Mamana Arif, ya Yara?" "Lafiyar su lau, ya labarin su Baba karami da su Maina?" "Suna lafiya lau " ta mai da hankalinta kan tv. "Badi'atul Noor ko zaki taimaka min da madubina a saman bedside" "tow " ta fada tana me barin falon, juyawa yayi ya zuba mata ido. "Me ya kawo ki? Ita tana muku haka ne? Tashi ki tafi" "babu inda zani wallahi sai ka kai mu umra kamar yadda kake yawo da ita." Kamar ya rufe ta da duka, ya rasa me zai ce don takaici. Dawowa Badi'atul Noor ya sa shi amsar madubin. "Ummin baba karami, ki saka baki ya biya mana umra fisabilillahi aiki babu adalci yana fifiko, ban da kowa yasan matsayin sa ai da Allah kadai yasan me zai faru. Wallahi Sultan baya mana adalci, idan ba zai iya zama da mu ba, ya sallame mu mana." Shiru tayi kallon ikon Allah. Ita da aka kora mata yaranta baki daya a gidan bata yi ihu ba. Murmushi tayi irin ta manya ta ce mata. "Shi kenan idan dai Umra ce ai kin kawo kuka inda ya da ce. Don Allah zaku ba iya umra ba har Dubai zaku." "Bani da kudi." Ya fada a gatsale. "Ah zan baka aro ko bashi." "Ba zan karba ba, na gaya miki bani da shi idan na samu zan biya musu su tafi lokacin Ramadan " "tow Allah ya hore maka" "Amin Ya Allah." Ya fada yana barin falon. Kallon Badariyyah tayi cikin tausasshen harshe ta ce mata. "In sha Allah zaku tafi, ki kara hakuri zan kokarta miki koda dukkan ku baku tafi ba, amma ke da yaranki zaku tafi." Gyada kai tayi tana faɗin. "Ya dai ji tsoron Allah, babu adalci a cikin lamarin shi " " a kara hakuri dai" haka tayi ta mita har ta bar falon, idan ta fahimta ita yake fifutawa akan su, murmushi tayi. Wucewa ɗakinta, tayi wanka da sallah shafa'i da wutiri tayi addu'a sannan ta wuce dakinsa. Yana zaune yana aiki. "Barka da hutawa." "Yawwa " zama tayi tana kallon shi. "Kin ga bana son rigima fadi abin da yake ranki" "ka biya musu Umra kawai a wuce wurin" "ai na gaya miki gaskiya bani da shi" "me yasa kake haka ne? Su gani suke ka fititani." "Eh su fadi abin da ya musu ma" "amma sai ka biya wallahi" "Badi'atul" "Na'am bani da shi" " Allah kana da shi ka biya musu kawai" "idan nace zan biya dukkan ku hudu zan biyawa." "Na yafe ka biya musu ai ni Yarana suna biya min." "Shi kenan zan duba" "ka kyauta" ta wuce ta kashe wutar dakin ta kwanta abin ta. Washi gari bayan yan sallah la'asar ya tura musu Ibrahim baban dan hajiya Mariyah ya amso passport dinnsu. Sai wurin isha da ya shiga cikin gidan ya bawa Sultanate takardun su, domin har da ita a a cikin masu zuwa umran. Ai kuwa saka albarka kamar harshenta zai tsinke da saka mishi albarka take. Ya mata sallama ya bar ta tana murna. Haka ta turawa matansa da suke karkashin inuwar ta, anan Badariyyah take musu burga da cewa ita tace mishi ya biyawa Sultanate Umra shine ya ce a'a su tafi tare, wayyo da tasan bala'in da ta jangwalo ba zata fadi haka ba, domin dai Sultanate ta ce bata zuwa umran tunda ita ta nima nata Alfarman zuwa ba shi yayi niyya ba, dama kuma tana da rikicin tsufanta yar batalikan nan ta haɗa kowa ta ci mutuncin sa. Dakyar aka samu ta sauko kuma abin dariya Badi'atul Noor din nan dai ita ce ta rarrasheta kafin ta sauko da sharadin sai dai su tafi abin su ita ta tafi aikin hajji da kyar aka kashe wutar suka tafi Umran. *After Four years ago* UK..... 08130269641 top-notch [03/06, 8:10 pm] usmanlauratu71: Shekaru hudu. _2013_ Ga Yaran Ummi kamar azaba ce, domin a cikin shekarun Abuturab ya farga da halin da Maina yake ciki, domin da farko ya manta yadda suka yi da iyayen su akan ya kula da Maina da suke ganin bai da lafiya, baki daya ya sha'afa sai shekara da suka wuce ya fahimci haka, sakamakon faduwar da Maina yayi a wurin aikin sa aka wuce da shi asibiti. Anan suka fahimci yana fama da mugun mura, da wasu kuraje masu tadda hankali. Duk yadda yaso daurewa sai da ya kasa, domin daga kirjin Maina zuwa bayan shi kurajen ne da suka watsa ƴaƴan su masu bala'in azaba da ciwo, amma karfin hali irin na shi haka yake kokarin ganin babu wanda ya gane, Allah ya taimaka lokacin da ya fadi Abuturab aka kira domin sun yi magana da Abuturab din ya fada, haka yasa aka samu last call din Maina. Koda ya zo asibitin shi kasa ya sha mamakin ciwon da magungunan da yake sha. Koda Maina ya fara abu daya ya nime Abuturab yayi ya bar maganar iya su, don Allah kar ya d'agawa Iyayen su hankali da matar shi da yan uwan su. Babu yadda Abuturab bai yi be yi ba amma haka Maina ya hana shi fadar ciwonsa. Tun daga lokacin Abuturab ya kasa zaune ya kasa tsaye wurin niman magani da haduwa da manyan kwararrun likitoci. Kullum cikin binciken ciwon Maina yake, haka yasa wani professor a Berlin na Germany ya bashi shawaran ya kai Maina Abubakar China domin suna da sani akan magunguna da ciwo, da wannan shawarar Abuturab suka tafi sai dai ance mai nima yana tare da samu, haka ce ta faru domin dai sun sami magani ba laifi amma kuma ba wai an san ciwon ba ne, sun ba shi magani da zai taimaka mishi akan rage radad'in da yake fama da shi, sai kuma na fatar shi, da aka bashi magani yana sha yana shafawa. Za a iya cewa Alhamdulillahi tunda dai har ya samu sauki babu laifi tunda lafiyar ce ta tabu dole sai a hankali sauƙin. Exactly shekara biyu kenan, a cikin wannan shekaru hudun duk shekara Zuwairah da Jalilah suka zuwa Nigeria ba don kome ba sai don dangin su, kuma a wannan zuwan da suke babu wanda ya tab'a sanin halin da Maina yake ciki, domin sun boye babu wanda ya sani sai shi da Abuturab. A gajiye Saraki ya shigo domin kwana biyu baya samun damar hutawa, har Asabar yana wurin aiki sakamakon yadda ake gab da yin bikin jikan sarauniyar Ingila. "Abuturab ina Maina kwana biyu bana ganin shi?" Hankalin shi yana kan aikin da yake s jikin laptop ya amsa mishi. " Ya tafi Beijing amma yau nake saka ran zai dawo" fitowa matar shi Aneesah tayi dauke da ruwan sanyi ta mika mishi, "Barka da dawowa ya aiki?" Ta amshi jakar aikin shi. Kurba yana kallon Abuturab. "Auta sai nake ganin kamar Maina bai da lafiya" da sauri Abuturab ya kalle shi, ya bude baki zai magana wayar tafi da gidan ka landline yayi kara, Aneesah da take kokarin shirya table saboda mijinta, ta dauki wayar. "Hello " "Muna magana da iyalan Mr Maina ne?" "Eh nan ne?" "Yana asibit ne bai da lafiya" "what?" Mikewa suka yi daga Abuturab har Saraki. "Ok ga mu nan zuwa " "wai Hamma Maina ne bai da lafiya ya fadi a airport amma sun wuce da shi asibiti " "innalillahi wa'inna illahi raju'un." "Muje kar ki bari Hamdiyah ta ji" suka fita daga shi har Abuturab, sun samu babu halin a shiga wurin shi, kiran Baban Latifah Alhaji Khamal... *** A cikin shekaru hudu nasara da cigaba an samu a rayuwar Sa'adatu Aminu Fulani, wacce take jerin daliban Ss1, yau saura kwana biyu bikin yaye daliban Ss3, don haka sosai hankalin su ya koma su da yan Ss2 da Ss3, abubuwan sun sha kan su, domin tun safe suka tashi sai dare suke komawa sallah da cin abinci yake dauke su daga wurin, saukowa tayi tana kallon Husnah da take kishingid'e kasar bishiyar da suke daura yadin zare kalar tutun nigeria. "Malam tashi mu tafi" lumshe idanu Husnah tayi, tana murmushi. Tashi tayi tana karkad'e jikinta. "Ina tunanin Ya muhsin ne!" Ta fada bayan ta zanen heart a hannu. Zaro idanu Sa'ade tayi tana b'ata yar karamar baby face din ta, tare da cizon lips dinta. Kyakyafta mata idanu Husnah tayi, tana tambayar ta me nene? D'aga kafada tayi tana juya idanun ta, (ana kiran salon wannan maganar da Morse code) ba kowa yake fahimtar ba, amma kurame suna yin shi musamman wadanda suka samu koyarwar shi yana da saukin isar da sakon da ba kowa yake fahimtar ba, a cikin daliban makarantar bai wuce su goma sha bakwai suka iya Morse code ba, a cikin daliban da suka fito da excellent Sa'ade ce ta biyu, sai wani Yaro ke bin ta sai Husnah. Rahilah da Kubrah cewa suka yi su Sign languages din ma ba kowa yake yi ba, sai masu saukin fahimta. Haka yasa iya su goma sha bakwai suke koyan lession din, wani abin da ba kowa ya sani ba. Shi kan shi Morse code yare ne na security agent jami'an tsaro sirri suke amfani da shi, musamman wurin isar da sakon da suke bukata, musamman idan aka kama su, kamar misalin idan yan ta'adda suka kama jami'an tsaro sirri, suka fito da su domin suyiwa gwamnati barazanar a sake su, tow kwararru a cikin jami'an suna iya isar da sako na musamman inda suke da kuma adadin mutanen da suke wurin. Ya samo asali ne daga wani Samuel Morse, shi yasa ake kiran shi da Morse code, sannan bayan haka yana da hanyoyi daddama wurin isar da shi, na farko akwai yin rubutun shi in alphabetical, sannan akwai yin amfani da shi da finger's, sannan akwai yin shi ga idanu. Waɗannan sune hanyar isar da shi. Yana da kyau. Wannan shi ne asalin yadda Sa'ade ta fara koyan yaren idan muka tuna farkon labarin inda take magana da idanu Inna Laminde ke iya fahimta, shi yasa da ta fahimci irin talent dinta, ta koyo hanyar fahimtar karatu da shi, sannan a bangaren ilimin Sign languages ma ba laifi tana kokari sosai, haka yasa baki daya ta daura ragamar tafiyar rayuwar ta akan. A hankali suke tafiya suna ratsa filin makarantar har zuwa hostle din su, Rahilah suka hango tana zaune saman barandar dakin su. Kubrah tana shan garin kwaki. Kallon su tai ta dauke kai tana tsaki. Haka ta gama cusa garin ta mike. Riko hannunta Rahilah tayi ta mata alamar ta zauna, idan ka zaka duba zaman su, hakuri suke da Kubrah don ma Rahilah bata daukar reni. Yanzu zata ci Ubanta a zauna lafiya. Dawo da ita tayi su fahimci juna. Wai fada aka yi akan Sa'ade, Kubrah da Husna duk shirun Husnah sai da ranta ya ɓaci tayi fada, sam Sa'ade bata iya rigima ba, sai dai idan tayi fushi abin baya kyau. Akan kayan abinciin Sa'ade ne da ya kare. Su uku kayan su a haɗe yake, suna haka ne saboda Rahilah haka Kubrah ta haɗa kayan ta da nasu, Ashe tana lura da kome da zarar kayan abincin Sa'ade ya kare ko Rahilah zata kwashe nata, dama na Sa'ade ake fara tab'awa tayi ta bakin hali kenan, dake tana masifar tsoron Rahilah da Husnah bata iskanci da renin hankali sai ta ga basu nan, tow nan zata yi ta bakin hali har Sa'ade tayi fushi taki cin abincin su. Rahilah da Husnah basu sani ba, sai yau da safe sun amso kunu Sa'ade ta bude locker zata dibi Sugar kawai Kubrah ta mike tana kallon duk abin da sa'ade take. Shine ta mike take tambayar ta "Meye yasa duk lokacin da zan debi abinci kike tsaya min a kaina?" Shi ne ta mike ta fara fada da ihu, kamar wani abu ya faru. Abin ya bawa Sa'ade haushi ta bar mata kunun da sigar zata fita suka hadu da Husnah tare ta, tayi tana tambayar ta lafiya? Shine ta fashe da kuka sosai har jikinta yana rawa. Ganin haka Husnah ta shiga dakin a fusace ta samu Kubrah tana raba kayan zata cire ta. Ai kuwa ita da ta fita hauka ta kwashe kayanta ta watsa mata su, ta rufe locker. Shine cikin fushi itama ta mike take nuna mata wato don tana gadaran ubanta me kudi ne shi ne zata watsar mata da kaya, akan wata yar kauye da iyayenta kauye suka fito, da ta daina kula Sa'ade da yafi ta bar sa'ade da Rahilah sune rayuwar su iri daya. Sake baki Husnah tayi ta ce mata. "Ban yi mamakin jin haka daga bakin ki ba, domin zaki fadi abin da yafi haka, ke ko kunya baki ji ba. Daga yau kar ki kuma shiga harkan mu ki je da halin ki. Barauniya kawai " shi ne fa dambe ya kacame a dakin dakyar Rahilah ta raba su bata san me ya faru ba, ita kuwa Husnah ta juya ta bar dakin. Tun da suka tafi take bin Rahilah sau da kafa saboda kar ta tambayi dalilin rigimar su , itama ta juya mata baya. Don sai da tayi fadar ta fahimci ba karamin son Sa'ade suke ba. Hango su da tayi, ba kome bane taburman kunya a nad'e shi da hauka tayi. Don kar a tadda zancen ne, su kuma sun manta sun yi fadar ma. Sa'ade tana shiga dakin su daukar bokiti zata yi ta gan shi cike da ruwa, kallon Rahilah tayi da take zaune. A gefenta tana murmushi. Dauka tayi zata fita Rahilah ta amsa mata, ta wuce ban daki ta tsaya a wurin. Har ta fito tana kallon ta. Sai da ta zo kusa da ita ta tambaye ta me ya faru ɗazun. Girgiza kai ta yi tana dariya ta mata alamar ya wuce a bar shi kawai.. *** Daga Hajiya Daulah ba zaka gane waye ya fi wani murnan dawowar Abdulhakim ba, sai ma yadda suke rawan jiki, dake shekara biyu da suka wuce Dr Sharif ya tura mishi ita, domin ta zauna da shi kafin a mishi aikin shi wanda ya rage saura watanin ne a mishi. Sai dai kuma bata kai wannan lokacin ba ta dawo gida, idan ta matso sai ta tafi wurin shi, har aka yi aikin. Ganin gari ba nasu ba, zata fara yawo ya dawo da ita tare da fadawa mahaifin sa kar ta kuma zuwa shi zaizo. Nan ma Hajiya Daulah ta cika tayi makil. Ko lokacin da za a mishi aikin karshe dole Dr Sharif ya ajiye aiki ba don kome ba, sai don rayuwar dan shi, sai da aka yi aikin har ya fara takawa suka dawo gida ya gama jinya yana gamawa ya lura zasu takura shi. Shi ne ya gudu inda ya fito. Yanzu ma abun da ya kawo shi bikin Afiyyah da za ayi kwanan nan ne, da kuma ya ga cigaban da kamfanin simintin Mahaifiyar shi yake samu, bayan nan ƙaddara ta kuma janyo shi izuwa sokoton Shehu..... 08130269641 Top-notch Addah Ramlat.... [05/06, 8:14 am] usmanlauratu71: Kamar mara gaskiya haka ya shiga cikin falon Hajiyar su yana yake, duk da dai lafiyar har zuwa yanzu sai godiyar Ubangiji, amma ba laifi, tunda rayuwar auratayyar shi da Sophia da sauki, domin daga yadda take rawan jiki zaka fahimci lallai kome lafiya lafiya, daga kan fuskar Hajiya Daulah zaka fahimci zallar farincikin da take ciki, musamman da suka yi ido biyu da Abdul din, wani yalwataccen Murmushi yake kwance a bisa fuskar ta, "Sannu Ubana,anya kaso dawowa kuwa?" Murmushi yayi yana me zama gefenta. "Hajiyata gani nan a gaban ki" "da ina fushi da kai amma yanzu na huce ya can inda kake? Ka bar min kamfanina sai a hankali. Amma Alhamdulillahi ya lafiyar ka?" "Alhamdulillahi hajiyata" ya faɗa kamar.me tsoron kar wani abu ya faru, don yasan hajiya wata birkitacciyar mace ce. "Ka je ka huta daga akwai maganar da zamu yi da kai mai muhimmanci ka ji" Hajiya Daulah tana lallaba shi ne saboda karfen da aka saka mishi a kirjinsa amma ba don haka ba, da ruwan masifa zata tarbe shi. Gidan sa ya wuce ya samu cike da yan mata kawayen Afiyyah. "Sannun ka da zuwa Ya Abdul" "Yawwa sannu ku Afi ya shirye-shiryen bikin?" "Alhamdulillahi, Masha Allah Ubangiji ya baku zaman lafiya" yana gama fadar haka ya wuce sama abin sa, domin Kawayenta kamar su cinye shi danye. Shi kuwa baya ciki da irin wannan kallon da suke mishi. A bakin kofar dakin sa ya hadu da Sophia. "Ina saurin na isa gidan Hajiya na dauko ka, ashe ka tawo?" "Eh gani" ya fada yana kokarin bude kofar, da dan sauri ta buɗe mishi kofar suka shiga. Yasan halinta yanzu zata iya damun shi. "Sophia" "shiiii, kayi shiru kawai It's my duty" ta fada tana taimaka mishi, har sai da yayi wanka tsaf. Sannan suka fito, itama a jiken. Fita tayi ta nufi dakinta, ta sauya kaya sannan ta nufi down stairs ta haɗa mishi abinci ta kawo mishi, idan ka cire azabar yawo Sophia bata da matsalar kome sai shegen yawo kamar wacce ya ci miyan shanshani. Kafin wani lokaci sun ci abinci an fada duniyar su iya su suke gane yanayin ko nace iya ita domin baki daya shi a bangaren shi baya wani dauki ko murnan haka. Wurin karfe shida suka sauko fess da su, wucewa masallaci yayi, Dr Sharif ya hango a kofar masallacin zaune rike da katin gayyata. "Sannu Abba, katin gayyata ne na bikin?" "A'a ƙatin bikin yaye daliban makarantar Raji special school ne" amsa yayi yana kallon katin. "Naga kamar jibi ne?" "Eh gashi nan sun gayyace ni" "Zan raka ka" murmushi yayi sannan ya ce mishi. "Allah ya kai mu" "Amin Ya Allah" *** UK.. Kallon Hamdiyah Alhaji Khamal yayi bako daya ya kasa yarda da abin da take fada. "Taya shekaru hudu mijin ki yana fama da ciwo irin wannan ki ce baki sani ba?" Cikin kuka ta ce mishi. "Na rantse da Allah ban sani ba, asalima kullum da rigar shi yake kwana" "Ina ga bai dace da ka tambaye ta irin wannan zancen ba, yayi nauyi da yawa" inji Abuturab da yake tsaye a wurin. Fitowar Latifah daga cikin dakin sa, kasancewar ta ɗaliba me sanin makaman aiki a bangaren likitanci, ta cire facemask ɗinta. A hankali ta saka a cikin aljuhun rigar labcoat. "Mimi ya dai?" Hàdiye yawu tayi tana faɗin. "A cigaba da addu'a" ta wuce Office din likitan da yake rike da case din shi. "Newbie's kin ga halin da yake cikin? Bana son na fad'awa familyn ki ne domin naga kamar kun fito daga Noble family." Gyada mishi kai tayi tana faɗin. "Eh daga Babban gida muka fito, wani hali yake ciki?" Mika mata x-ray din yayi yana faɗin. "Huhunsa dukka biyu sun lalace, shi yasa yake haki, dalilin da yasa kurajen da suke wurin hakarkarinsa kenan suka feso." Hàdiye yawu tayi cikin wani irin tsoro. "Me ke kawo ciwon?" "Eh toh sai dai mu tsannanta bincike, domin dai ban ga wani abu ba." "Please doctor kayi wani abu, shi ne next Crown princes" rike bakinsa yayi sannan ya ce mata. "Oh My God, bari na tura lab a diba mana ruwan ciwon hakarkarinsa da kuma jinin sa." Mikewa suka yi, suka fita baki daya, kafin kace me an dibi jinin an fita da shi. Daga Abuturab har Saraki da Alhaji Khamal. Suna tsaye a wurin sai shiga da fita su Latifa suke. Fitowar da Latifah tayi cikin mutuwar jiki ta kalle su. "Ku shiga wancan dakin zaa baku kaya ku saka sai ku shiga yana son magana da ku." Tana gama fadar haka ta wuce. Tana share hawayen da yake zubo mata. Riko arm dinta Abuturab yayi domin ya lura da yadda take kuka. "Gaya min meke faruwa?" "Babu kome Hamma" ta juya zata tafi ya kuma janyota suna kallon juna. "Me yasa mu Abubakar?" "Kaje yana son ganinka karka b'ata lokaci" "Mimi gaya min meke faruwa?" "Please ka kyale ni mana" ta kwace rikon da ya mata, ta zura da gudu. Ai bai tsaya sauya kaya ba, ya wuce dakin. Idanun Maina yana kan kofar, hannun shi cikin na Saraki. "Kayi hakuri Saraki ka kula min da kanka" ya fada yana rike da hannun shi. Juyawa yayi yana kallon matar shi. "Idan kika ji kewa da maraici akwai Saraki da Abuturab, akwai Rumaisah da Zakiyyah, da Ummy Aymana, ga Ummin mu da Abban ki. Ba zasu tab'a barin kiyi maraicina ba." Wani irin kuka ta sake tana me juyawa zata fita. "Auta baka saka kayan kariyar ba? Zo auta ina son baka wani matsayi na musamman. Ku bamu wuri" ya fada yana tari. Rike shi Saraki yayi. "Ku bamu wuri babu Ummin mu auta zo nan kafi mu jin duminta zo ka bani jikinka naji dumi" wucewa yayi Alhaji Khamal ya bashi facemask ya saka, mika mishi hannu Maina yayi, ya d'an d'aga shi sannan ya zare pillow da yake kai, ya jingina Maina a jikin shi. "Hammmm" ya sauke ajiyar zuciya. *** Kwara. Barcin la'asar kowa yasan babu kyau, ita kanta Ummin ta sani, amma yadda barci yake cin idanunta kamar ta kwana bata yi ba. Asalima yau tun tashinta da suka yi waya da Maina yake mata wasu irin magana. Takaici yasa ta kashe wayar. Tun safe bata kuma jin duriyar kiran shi ba, shi ne ta kira Saraki ya tabbatar mata baya ganin shi kwana biyu. Ai kuwa ya sha fada kamar ta shiga wayar. Har yamma tana kiran su layikan su a kashe. A hankali barci yayi gaba da ita, tafiya take ta gefen makabarta, ta ga an tone kabari biyu, ana shirin tone na ukun ta isa wurin tana tambayar su. "Kabarin su waye haka tonawa?" Juyawa mutanen suka yi daya daga ya ce mata. "Ga me kabarin can zuwa" juyawa tayi itama tabbas ba gizau bane Maina ne sanye da farin jallabiya, sai sauri yake, Saraki yana bin bayan shi a hankali kamar baya son zuwa, shi kuwa sai sauri yake kamar zai tashi sama. Yana isowa ya kalli Ummin su ya ce mata. "Kin ga yayi miki kyau ko? Kin ga yadda labarin yake, gaskiya yafi ko ina kyau da aminci. Ummina na gode sosai bari na kwanta." "Innalilahi wa'inna laihil raju'un Ubangiji ka raba mu da mugun ji da mugun gani." Ta farka tana zufa kamar wacce tayi gudun faffalaki. *** UK.. Fita suka yi suka basu wuri, "Abuturab don Allah ka roka min Ummina da Abbana su yafe min, ga Annur da Nur, kasan wani abu? Duk da wannan yanayin na jinya she is pregnant. Naki barin ta fahimci ciwon ne domin bana cire kayana, kome na kamar mara gaskiya nake yi, duk da naso na sake ta, sai dai tana bani tausayi. "Abuturab kayi hakuri zan tafi na barka da nauyin da ya dace na dauka." Ya fada yana kwantar da kan shi a kirjin Abuturab. Tari ya fara sosai yanayi yana amai kamar zai juye kayan cikin sa, sai kokarin aman yake. "Bari a kira likita" "girgiza kai yayi sannan ya rike Abuturab. Yana wani irin yunkuri, haka yaui ta aman guda-gudan jini, yayi yana rike hannun Abuturab da karfi kamar zai balla mishi kashin hannu, "La'ilallah halillah Muhammad Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama." Shi ne kalmar da yake fada yana nanatawa, Abuturab yana taya shi. Yanayi yana firgita, yanayi yana kara rike dan uwansa, rungumar shi sosai Abuturab yayi ko ba a gaya mishi ba, yasan yau Abubakar yana amsa kiran mahaliccin sa, a hankali yake jin wani irin tsoron Allah, yana shiga cikin zuciyar shi, imani da Allah yana kara samun muhalli a cikin kokon tanshi, a hankali yake kallon yadda Abubakar Maina yake shure-shure yana salatin, kafin ya shiga maimaita kalmar shahada, a hankali Abuturab yana taya shi har ya daina jin muryan shi, sai dai al'amar yana yi, karshe ya daina ganin alamar ma. Sai dai ya dauki lokaci yaji ya sauke ajiyar zuciya, jikin shi yayi nauyi. Rungumar Maina yayi sosai cikin wani irin kewar dan uwansa, soyayyar dan uwan yana kara cika mishi zuciya, yau itace farkon da yaga mutuwa a idanun shi, mutuwar ma ta dan uwan shi. A hankali ya kwantar shi, sannan ya gyara mishi kwanciya ya rufe mishi idanu, kafin ya kofar fita suna kallon shi yadda jikin shi ya b'aci da jini. "Aliyu!" Saraki ya kira sunan shi. Kallon shi yayi a hankali ya nemi wuri ya zauna. Ciro wayar shi yayi, yana ganin Latifah da sauran likitocin zasu shiga dakin ya ce "da kun koma ya rasu ma" ya fada yana saka wayar shi a kunne kamar ba shi yayi maganar ba, ko mantawa yayi ne, sai jin faduwar Hamdiyah suka yi. Baki daya ya manta tana wurin, da idanun ya bita da shi kamar yana kallon sabuwar halitta, ya ce. "Latifah ku kaita maternity ciki ne da ita" kafin ya mai da hankali kan wayar. "Abba, muna hanyar zuwa don Allah ka lallaba Ummin mu, Abubakar ya amsa kiran mahaliccin mu, please ka lallaba Ummi." "Innalilahi wa'inna laihil raju'un Ubangiji ya Jikan Abubakar Maina, Ina Saraki?" Sun wuce da Hamdiyah maternity in sha Allah gobe zamu taso jibi zamu iso kasan gawa ce dole sai an cike cike" "Allah ya maka albarka, ka tsaya akan kome Aliyu " "shi kenan Abba" kallon Alhaji Khamal yayi yana faɗin. "Abba mu karasa sauran abubuwan da ake bukata " mikewa suka yi shima Baban Latifah jikin shi yayi sanyi. Haka suka ta shige da ficce, aka tura gawar mutuare, sannan suka wuce Office din Embassy na Nigeria dake nan British, suka gama kome, airport suka wuce aanan ma sai da suka dauki lokaci. Kafin suka dawo gida, kusan duk yawon da suke a babu wanda ya samu arzikn cikin abinci, sai jigila kawai suke akan yadda za a fitar da gawan zuwa Nigeria. *** Bayan sallah ishe Sultan ya isa falon Sultanah da take kwance akan abin sallah. Zama yayi yana kallon ta. Kafin ya zauna shima. "Tunanin me kike ina ta sallama?" Tashi tayi zaune tana murmushin karfin hali domin jikinta baki daya babu kwari. "Ina tuna ranar da na haifi Maina ne, sai da yayi kwana uku bai sha nono ba, saboda daga ni har shi bakin juna ne. Ranar da ya fara sha, ina kuka yana sha. Baki daya abin dariya yake bani" matsawa yayi jikinta sosai. Ya riko hannunta, "eh haka al'amarin, musamman da yazo lokacin ana rikicin ba a sona" murmusa mishi tayi, sannan ta zare hannunta zata kwanta. "Badi'atul Noor" bude idanu tayi tana kallon shi. "Waye ya halicce ki?" Bakinta yayi matukar nauyi ta ce. "ALLAH" "su Ƴaran ban waye ya baki su?" "Allah" "Ina iyayen ki?" "Allah ya amshe su?" "Idan Allah ya amshi abin da ya baki ya zaki ji?" "Da zafi kan amma kuma ai shi ya halicci kayan sa, kuma Ya bamu aron shi ya kuma karba a lokacin da yaso, babu amfanin tashin hankali sai dai muce tsarki ya tabbata ga makagin halittun farko da ba karshe." Rike hannun ta yayi. "Alhamdulillahi, Allah ya amshi Abubakar Maina." D'ago kai tayi tana kallon shi, wani irin zazzaɓi ne ya rufe ta, bata san lokacin da ta sulalle kasa ta kwanta ba, "Badi'atul Noor." "Ba kome zazzaɓi nake ji, dan rufa min bargo" ...... *In sha Allah zuwa dare zan kara muku. 08130269641* [05/06, 6:59 pm] usmanlauratu71: .Kamar wacce aka lullube ta da danyen nama haka take jin ta, baki daya kanta wani irin juyawa yake, kafin taji har cikin Idanunta juyawa yaƙe. Rintsa idanun tayi da karfi tana faɗin. "Maina ya rasu ka ce min ko?" "Eh Badi'atul Noor" ajiyar zuciya ta sauke tana faɗin. "Alhamdulillahi" ta kuma lumshe idanunta, na wani lokaci kafin ta bude ta ce mishi. "Yaushe zasu iso?" "Jibi in sha Allah" murmushi tayi, ta kwanta a wurin. Wayarta ne ya fara kara, ya dauko tana ji amma bata da wani kuzarin daukar wayar. Ummy Aymana ce ta fara magana cikin kuka."Ummin mu Hamma Maina" "ba ita bace." "Abba Hamma Maina ya rasu" "ki mishi Addu'a" daga haka ya kashe wayar duk tana jin shi, kafin kace kwabo labarin mutuwar Maina ya kara watsuwa cikin Masarautar, jikin kowa ya mutu, mutum me hakuri da sanin darajar na kusa da shi, Maina bai da abokin fada babu ruwan shi da fankama da dabi'un yaran sarakuna. Yana da kirki sosai kamar me ga iya mu'amala da mutane. A hankali barci yayi gaba da ita bayan zazzaɓin ya saukar mata a falon Sultan yayi Sallah isha, ana idarwa Rumaisah tana shigowa, can sai ga Zakiyyah, bata zauna ba Ummy Aymana ta shigo itama, suka saka mahaifiyar su a gaba suna kuka, sai da Sultan ya musu nasiha sosai, kafin suka daina kukan. Suna zaune a wurin Sultanate ta shigo, duk kiyayyar ta da Ƴaran Badi'atul sai da ta yi kuka musamman Maina da yake da hakuri duk abin da tsanar su da take, bai hanata kuka ba. "Ayya mutuwa me yasa zaki dauki bawan Allah ko bar mutanen banza? Mutuwa me yasa ba ki dauke marasa kunyar dakin Badi'atul Noor ba?" Babu wanda ya kulata, kafin wani lokaci dakin Ummi ya cika sosai da jama'a har wurin goma na dare kafin aka watse. Sai wurin karfe biyu Ummin ta farka, ta zauna tana kallon yaranta da suke zaman gadinta. A hankali ta tashi zaune ta zuba musu idanu. Wani abu ta ji ya taso ya tsaya mata a kirjin ta, fiyye da yadda bata tsammani ya tsaya mata, a hankali ta zare jikinta zuwa ban daki, kunna ruwa yana zuba a tsakiyar kanta. Kuka take son yi amma ta kasa yin kukan sai ma jin wannan abin da ya mata bake-bake. Haka tayi wanka da alola ra fito , sannan ta shimfida abin sallah. Ta sauke Isha da yake kanta da shafa'i da wutiri. Tana idarwa ta zauna a wurin baki daya wani irin tausayin shi take ji, tausayin d'a da Uwa, tausayin irin na jin kan D'a da uwa, har lokacin so take tayi kuka domin zuciyar ta kamar an hura mata wuta ne, tana zaune a wurin tsawon daren gani take kamar gari ba zai waye ba, a rayuwar ta bata tab'a ganin dare mai tsawon wannan daren ba, abu daya yake yawo a ranta, shi ne ranar da ta haife shi, yadda aka daura mata shi a kan cinyarta. Abu na biyu ranar da ya fara shan nono, abu na uku ranar da ya fara mata dariya, wadannan abubuwan bata iya mantawa da su har ta koma ga Allah. Ba zata iya manta su ba, har ta daina numfashi. Anya akwai abin da ya kai mutuwar D'a girgiza? Bayan na iyayenta bata ji mutuwar da ya hana ta barci ba, sai mutuwar. Ko ta lumshe idanunta Maina take gani yana dariya, baki daya zuciyarta a cushe yake da dinbin tashin hankali, so take taji ko da gaske ne, mutuwar ce, yakushin kanta tayi, ta ji zafin a fatar da ranta. "Alhamdulillahi" ta furta, yadda ta ga rana haka ta ga dare, wurin uku saura ta tashi zuwa ban daki ta kuma dauro alola taso ta fara nafilla har aka yi aka kira sallah farko, ta gabatar da raka'atul fijr, tana cikin Addu'a, su Rumaisah suka farka ganinta kan abin sallah ya basu mamaki, amma basu yi mamaki ba domin ita din Ma'abociyar ibada ce, haka suka wuce kowacce tayi alola ta fito suka yi sallah, kafin suka juya gare ta. "Ummin mu ina kwana? Ya karin hakuri Allah ya mishi rahama!" "Lafiya lau, Alhamdulillahi Amin Ya Allah " ta fada fuskar ta a sake, haka suka mata ta'aziyar dan uwannsu sanan suka zauna har gari ya fara haske kafin suka kama aikin gyaran ɗakinta, Rumaisah ta wuce kitchen din da yake saman ta mata abin karyawa. Tana aikin ta ji muryan Abban su, ya shigo katse kome tayi ta fito ta Gaishe sa. Sannan ta koma tea tayi da pan cake,ta kawo ɗakinta Ummin, ya ajiye mata. Har lokacin abban su yana falon suna tattaunawa akan zuwan su. "Ina ga ayi jana'izar shi a fada kamar yadda akewa kowa, domin waziri ya bukaci idan aka kawo shi ayi wani binciken, ni kuma ina ganin a bar shi kawai a mishi suturan shi a wuce da shi gidan shi na gaskiya" kura mishi idanun tayi kafin ta ce mishi. "Ban gane ayi wani binciken ba, dama jinya yayi ne?" Gyada mata kai yayi, cikin sanyin murya ya ce mata. "Jinya yayi sosai tsawon shekaru huɗu yana jinya tun komawar Abuturab can." A hankali ta janye hannunta cikin nashi ta kura mishi idanun kafin ta ce. "Allah ya gafarta mishi yasa jinya ta kankara zunubi" "Amin Ya Allah " haka ya mike yana kallon ta. "Zauna ka karya mana" ta ce mishi, girgiza kai yayi, yana murmushi. "Bana jin yunwa" sai a lokacin ta lura da wani irin rama da yayi fuskar shi ta fitar da tsufar shi abin da da bai da shi, haka ya fita kamar wanda aka mishi duka. Can wurin karfe goma Sultanate ta shigo tana kallon Ummy Aymana da take saka turaren wuta. "Sannu sara me bakar takashi, so kike na gaishe ki?" Banza da ita Ummy Aymana tayi tana cigaba da aikin ta. "Dama kune kuka mutu aka bar min Buba Maina" "idan bamu mutu ba, sai ko.kashe mu yar renin hankali" ta fada kasa-kasa. "Kika zagi uwata Aimana?" Sultanate ta fada cikin d'aga Murya salon kowa yaji abin da ta fada. "Kyaji da halin ki" "innalillahi wa'inna illahi raju'un, wayyo Allah na yau ni ake zagi ko tausayi min rashin Buba maina yar nan bata yi ba take zagina ciki da waje." Ta fashe da kuka, "Aymana me yasa baki jin magana.ne? Baki ga halin da ake ciki ne? Fisabilillah sai kin saka jinin Ummi ya hau ne?" "Tow Didih don Allah me na mata? Ta gaya muku me na mata?'" wani kallon banza ta watsawa Sultanate, ta wuce. "Kuyi hakuri Sultanate " "Ai dole nayi tun da Buba Maina ya mutu sai ku min abin da ranku yake so, shi daya ne yake sona da gaskiya wayyo mutuwa me yasa baki dauke ni ba" ta fada tana rushewa da kuka, maganar gaskiya mutuwar Maina ya daki Sultanate, duk da tsanar da take mishi bata kawo cewa zai tafi very soon ba, ita kawai tafi ganin cewa gara ta nisan ta su ga thrones na masarautar sama da ta tab'a lafiyar su, duk da takun sakar da suke yi da Uwar su, duk abin da Sultanate tayi Maina Uzuri yake mata, ya kance soyayyar danta ne yake janyo take musu wulakanci da cin zarafin su, yana yawancewa akwai wani boyayyen al'amarin da Sultanate tayi yasa take tsoron kar ya shafe su. Shi yasa take kare danta, sannan ya tab'a gayawa Rumaisah cewa Son da take musu yasa bata son ganin suna cikin masarautar domin za a iya cutar dasu saboda mahaifin su, ta gaya mishi haka ne lokacin da ya je mata sallama zasu bar kasar. Ire-iren waɗannan abubuwan yasa take kin su, duk da ta sha gaya mishi. "a duk lokacin da kasan laifin da nayi da hannunka zaka kashe ni har lahira kafin hakkin ya fara bibiyar ku, domin nasan ba iya kaina da Mahaifin ku zai tsaya ba. " Hawaye ne ya zubo daga idanun Rumaisah tunawa da tayi da kalaman sa, tabbas akwai wani abu da yake faruwa a cikin masarautar tun.kafin a haife su, "tow meye shi?" Kalaman Sultanate taji tana faɗin. "Allah na tuba, Allah ka yafe mana" *** Colleague na wurin aikin Maina su. Zo da boss dinsu, musamman yan uwa musulmai da suke aiki tare, kowa ya ji mutuwar shi. Haka gidan baya ya kasance da masu zuwa gaisuwa. Tun ranar da ya rasu Likitan da yake kan shi ya kira Latifah da dadare ya bata file din ciwon Maina, ra firgita kamar zata mutu, tsoro ya hanata sakat wani abin da ya kara furgitatta shi ne sakon da ake turo mata. *Nasan zuwa yanzu babu wanda yasan ciwon da ya kashe Maina! Ki kula da rayuwar mahaifin da ta Mahaifiyar ki, ko na shi wanda kike Haukar kina, ko ita Badi'atul Noor bata wuce ayi lomar tuwo da ita ba, balle ke kiyashi. Ki kona file din nan awa 72 kafin ki shigo nigeria ko kuma hmm Yarinyar zaki gani da idanun ki, layin ya fara sauka akan Maina ko waye next?* Ta matukar kaduwa da ta ga sakon hakan yasa taki haduwa da kowa gani take kamar ma zasu fahimci barazanar da ake mata shi yasa taki fitowa. *** Sa'ade tunda suka gama jarabawar su, Yusuf ya zo ya tafi mata da kayan ta, sauran ya bari ranar da suka yi hutu sai ta tawo da sauran. Yasa baki daya take takure. Don ma tana amfani da kayan Husnah da Rahilah, wani irin soyayya suke mata, kuma babu hassada ko Kyashi zaman su akwai dadi da fahimtar juna, ganin Kubrah zata kawo musu rigima yasa suka watsar da lamarin ta, gobe ne bikin yaye daliban aji shida, yasa suke ta kintsa kayan su, saboda su ranar zasu bar makaranta, yayinda wasu sai juma'a. Haka suka yi ta shiri ba, gefe guda wasu sun kafa hira wasu gulma. A cikin yan gulma har da Kubrah. Ganin tun shekaran jiya da suka yi fada da Sa'ade bata kuma shiga harkata ba, yasa ta koma gefe tana zaginta Ita da wasu Kawarta me suna hajiyayye. Ita kanta Hajiyayyen ba wani abin arzikn yake haɗa su da Kubrah sai cuta, domin kuwa kwashe mata kayan abinci take da wayo, wai a haka tafi su Sa'ade kaunarta.... Top-notch 08130269641 [06/06, 8:36 am] usmanlauratu71: 29.. Ganin yadda ta sauya tsarin Rayuwar ta, yasa suma suka watsar da ita, washi garin da za ayi taron tun wuri suka gama shirin su, daga nan wurin taron zasu wuce gidan su Husnah, domin yawo zasu yi kafin raka Rahilah gidan su. Daga nan ta wuce gida itama, sai dai wannan karon tayi alkawarin zata Maikulki ganin Innarta ta gaji da zaman sai tazo ganin ta. Komawa yayi ta kwanta tana dafe kanta. Tab'ata Rahilah tayi tana tambayar ta lafiya? Yar karamar murmushi tayi sannan ta mike zaune tana dafe kirjin ta. Janyo jakar makarantar ta, tayi ta zuge zip din. Wani littafi karami pink colour me zanen butterflies, sai hoton daya daga cikin barbe tana tashi sama. Dariya suka fara mata, bude littafin tayi ta zaro pen din da yake zuwa da littafin ta, ta fara rubutu cikin gangariyar turanci akan wasu yanayi na shauki da take ji, tare da matsanancin kewar Hamma Abuturab da take kwana da shi take ta shi da shi. ```'I feel bad' I feel like crying in vain, I don't know how to end this pain, coz I am missing you so much, your words and your thought, please come back in my life my dear, I really don't have any reason to cheer, please come back oh dear!``` kwace littafin Husnah tayi, ta ware idanun tana kallon Rahilah ta juya tana kallon ta, hawaye ne ya cika Idanunta, ta fita da gudu tana shaƙar iskar da yake kad'awa, lumshe idanunta tayi tana shaƙar iskar, haka kawai take jin kuka da kuma farin ciki mara iyaka. (🤣😂😹 Yanzu sai su kwashe min albasa me lawashi😭😂 i found love) fitowa Rahilah tayi tana me riko hannunta. Suka dawo cikin dakin. "Da gaske kin yi missing din shi har haka ne? Ko dai ko dai?" Zare idanu tayi tana girgiza kai, alamar a'a ba haka ba ne, da hannun Husnah tambaye ta, "tow meye nufinki na rubuta wannan tsadaddun kalmomin masu tsada da kwarjini, ni kin sani ma na ji ina son na ruhutawa Ya Muhsin " sake mata duka Rahilah tayi akan cinya tana nuna musu lokaci ya tafi, a wrist watch ɗinta. Mikewa tayi domin sha daya ake nima, suna shirin fita Kubrah ta shigo ita ɗaya, ta cancad'a kwalliya kamar zata wani wurin biki. Babu wanda ya ce mata, tattara kayan su, suka yi a wuri guda suka rufe sannan suka fita. Suna hira. *** Karfe sha goma da arba'in da tara, jirgin Maxi air, ya sauka babban airport din Lagos. Sanye yake da wando kaftani sage green sai rigar jamfa ce Ivory colour, hannun shi na sweater coat, kasancewar sun tsaya a Island, sakamakon matsalar da jirgin taso samu, haka suka nime kayan sanyi domin yanayin garin akwai dan ƙaren sanyi. Hannun shi na hagu rike da Annur, a hankali kowa yake saukowa, suka nufi inda zasu zauna su jira jirgin da zai wuce da su kwara. Idanun shi toshe yake da bakar madubi na sunglass, ya saka ne domin hana mutane gane halin da yake ciki ba. Wurin karfe sha daya da rabi aka fitar da gawar Maina aka mai da ita cikin jirgin da zata wuce da su, sai da aka gama shiri sannan suka dauki hanya zuwa kwara, idan ka ga yadda jikin su yayi sanyi musamman Saraki da yake jin kamar bai da lafiya ta cikinsa. Sai Hamdiyah da take ta kuka, gwanin ban tausayi, wurin karfe aha biyu da arba'in da biyar suka isa kwara, manyan jami'an gwamnati da manyan a cikin emirate council suka zo taran su, har suka isa fada garin ya cika da mutane. Kafin ka ce me an samu an shigar da gawar Falourn Sultan. Akan lokaci likitoci da forensic suka shiga nasu binciken. A can bangaren Sultanah Badi'atul Noor, tunda Hamdiyah ta shigo ta kwanta a jikinta tana kuka tana faɗin. "Ummina na zama marainiya, Maina shi ne Uwata shi ne Ubana, shi ne abokina bani da kawa sai Maina, Ummi Maina ya tsaya min nayi achieve din abubuwa, yana shirin kara min kwarin gwiwa ya mutu, Ummina Yaran mu" "Allah yana sane da Al'amarin ku" haka tayi ta shafa bayan ta, lokacin da Abuturab ya leko dakin ya cika makil, daga nesa ta hango shi, murmushi ta sakar mishi na kwarin gwiwa. A can Falourn Sultan kuwa, waziri Dawud ne akan binciken ana gamawa ya saka a briefcase dinshi ya cire babban rigar shi ya nad'e kafar wandon shi da hannun rigar shi, tare da Saraki. Zasu wanke gawar Sultanate ta shigo tana kuka da kururuwa. A bayan ta Abuturab ne. "Ya isa haka mamaci bai son kuka da kururuwa." "Ungo naka nace maka dan banza mara kunya yo ai da kai ka mutu ko kuka ba zan yi ba" yasan duk da tsufa da rikici amma baya tunanin ko gawar sa ta gani sai tafi haka haukacewa domin wallahi asalin rigimar su da fadar su soyayya ce, laifin yadda Ummi tayi ta haihuwa su maza ne yake bata haushi. Domin da jimawa sun yi haka da ita, da ya ce mata. "Wai ke me yasa kika tsane mu?" "Banza halin uwarka da tayi ta zazzage ku maza uku, ina laifin tayi maza biyu Allah ya raya su, shine don munafinci ana son a kashe min Yarona shi ne ta haife ka da idanun a tsakar ka." "Kina nufin zuwa na ya hanaki rawan gaban hantsi ne?" "Dan banza mara kunya, kai ban da kana da sauran shan ruwa ai da ka jima da mutuwa dan farka me rantalelan kai" ajiyar zuciya ya sauke, fitar da ita yayi tana kuka tana dukar shi. Haduwa suka yi a hanya da su Abdulrashid da Hajiya Suhailah sai Yarta autar ta Sahra. Kallon juna suka yi na wasu dakikai. "Aliyu ya hakuri" "ungo naki Suhailah ai ko babu kome kya kira shi da Baba karami, tunda sunan Uban Mijinki ne." Shiru tayi bata kula Sultanate ba, "Abuturab ya hakuri, ashe kuma Maina ya tafi?" "Eh wallahi Babban Yaya " ya ja hannun Sultanate. "Baby prince ya hakuri? Ashe Hamma Maina lokaci yayi." "Eh Sarah " ya fada yana barin wurin. "In ji Hamma Abdulkarim wai na mika maka sakon ta'aziyar shi, in sha Allah zai zo kafin ayi Seven " "Allah ya kai mu, Allah ya kawo shi." Haka ya kai ta ɓangarenta, sai kuka take. "Kin gan ni ba zan iya rarrashin ki ba, wanda yake rarrashin ki kenan ya amsa kiran mahaliccin sa, don haka ki daina kuka domin ba zan yarda ji daurawa Abba wani damuwa ba. Ki kula da kanki " takaici yasa ta rufe shi da duka, jikinta yana rawa. Tabbas mutuwar Maina ya girgiza Sultanate. Ba zai ce ba amma kuma yadda ta firgice abin yana bashi mamaki da daura ayar tambaya akanta. Mikewa yayi zai fita ta riko hannun shi. "Kar ka sake ka yarda da kowa, ka gayawa Saraki kar ya ci abincin kowa ko ya sha ruwan sadaka, idan kuna jin yunwa ga wannan key din store na ne" kallon ta yake cike da mamaki yana kuma kara jin wani abu a ransa. Durkusawa yayi a gabanta ya zuba hannun shi akan gwiwar ta. "Me kika nufi?" "A'a bana nufin kome ka san dai abin da yake faruwa a gidan nan kawai ku kula da kan ku." Haka ya mike tare da ajiye mata key dinta a kan cinyarta. "Ga kayan ki." Ya juya ya fita. Ba tare da ya kuma mata magana ba, domin hankalin shi ya koma kan Saraki. Yana zuwa falon Sultan ya samu sun gama wanka ana shirya shi Abdulrashid yana goge falon, koma cikin gidan yayi ya dauko turaren wuta aka saka a falon, lokacin an gama shirya gawan. "Saraki jeka dauko mahaifiyar ku da matar shi, da matar shi." "Tow Abba " har a lokacin Abuturab na kallon abin kamar a mafarki. "Abuturab ko zaka dauko mana Sultanate ne?" "Abba kyale ta depression zai mata yawa domin kusan sai a hankali kamata yayi a tura mata likita ya duba ta." "Kaci kaniyar ka, gani da kafana ba dawo. Wai ni mutuwa me yasa baki dauke dan banza me taurin zuciyar nan ba, kika dauke Buba Maina." Ta fada tana sakar mishi duka a baya, zuwa tayi ta zauna a gaban gawan Maina. "Buba Maina haka min ? Haka zaka min baka zuba min kasa ba, nice zan zuba maka kasa? Buba Maina me yasa zaka tafi lokacin da Badi'atul da Abdurrhmanu suke buƙatar ka?" Ta fada tana kuka, jikin kowa yayi sanyi domin kuwa kowa yasan yadda ta tsani Yaran Badi'atul Noor. Shigowar su Ummi, yasa ta kallon su. "Sannu Badi'atul Noor." Murmushi Ummin tayi tana isa kan gawar Maina, dafa kan shi tayi tana mishi Addu'a, tana gamawa ta sumbaci goshinsa. "Abubakar Ubangiji ya amshi bakuncin ka, Rabbana ya haskaka ya haska kabarin, Allah ya baka ikon amsa tambayoyin ka, Ubangiji ya raba ka da azabar kabari, Ya Allah nayi tawassali da sunayenka tsarkaka ka jikan Abubakar ka mishi rahama, ka yafe Mishi kura-kuran sa. Ya Allah ga bawan ka nan" ta fada haka, mikewa tayi ta ce. "Ina ga sun gama ku mika shi makwancinsa na gaskiya " tana fadar haka, wani irin duhu ya lullube idanunta, Allah yasa Saraki na bakin kofar, yadda ta jefa kafar ta, sai komawa tayi zata fadi, baki daya Yaran suka tare uwar su, da sauri Suka kwantar da ita. Numfashi ta yana sama da kasa. "Ku kai shi gidan shi na gaskiya" "Ummy Aymana ina kayan aikinki" Saraki ya tambaye ta, "yana sama bari na dauko" shigowar Latifah, dama yadda ta ga Ummin ta fito daga falon ta, tasan za ayi haka. Shi yasa da ta ji an bakin kofar na faɗin Sultanah Badi'atul Noor ta fadi ta koma ta dauko kayan ta, akan lokaci ta shiga kokarinta, baki daya Ummy Aymana gani take kamar bata taɓa rike ko da safar hannu ne, baki daya ta rikice ta fice, fita da gawar Maina aka yi a falon, aka tafi jana'izar shi, "Saraki muje da kai, Abuturab ka koma ka duba su idan da hali ku wuce asibitin." Duk yadda yaso yaga kabarin Maina haka ya hakura, yana zuwa yaga babu wani cigaba shawara ya basu aka wuce da ita asibiti. (Ya Allah ka jikan iyayen mu da sauran al'ummar Musulmi baki daya) *** Wurin sha biyu aka fara taron, Tsohon Kwamishinan ilimi, Dr Sharif ya samu halartar taron tare da Abdulhakim. Ana cikin taron wayar Abdulhakim tayi ta ruri dole ya fita daga cikin rumfar ya nufi wajen makarantar. A hankali yake takawa yana duba me kiran shi, kasancewar makarantar babu kowa ana can wurin taron, irin bugawa karfen da yake kirjin shi yayi, a hankali ya rike wurin tare da durkusawa kasa, yana haki jini ne ya shiga fita ta hancinsa. A hankali ya sulalle kasa ya fadi. Sa'ade ta fito daga hostle saboda mantuwa da tayi ta koma ta dauka, tana son ta koma inda suke zaune, har ta wuce shi sai ta kuma dawowa, a hankali ta isa kanshi, tana kallon shi. Dishi -dishi yake hangota. Sake bude idanun yayi tana girgiza kai. Dulum ya daina ganin a hankali ya rufe idanun shi. Wayar shi da ta gani a yashe shi ta dauka. Ta fara juyawa shi bata san yadda ake amfani da shi ba, kira ne ya shigo wayar baro-baro ta ga an rubuta My Super hero. Da sauri ta katse kiran ta shiga call din, sake kiran aka yi ta katse, tunda bata da yadda zata yi magana, sako ta turawa layin. *Wannan me wayar gashi nan yayi collapse* ta tura da sauri. Can aka kuma kiran shi. Katsewa tayi ta ce. *yana harabar makarantar ba zan iya magana ba* can kuwa sai ga wasu daga cikin malamai da shi kan shi tsohon Kwamishinan ilimi, tana durkushe a gaban shi, isowa wurin suka yi. "Sir bai da lafiya ne?" "Ina ga" godiya suka mata, Malam Dalhat ya tambaye ta yadda abin ya faru ta gaya masa, shi ya musu bayani, sannan suka sallame ta......08130269641 Top-notch 🙄 🚶🏽‍♀️🚶🏽‍♀️😹🤣😂😹😂 Chaiiiiiiii ye... Mu hadu a intermission babu dual typing daya ne kawai Yasin [07/06, 10:53 am] usmanlauratu71: 30... Sam ita bata dauki abin da ya faru da wani babban al'amari ba, domin ita abin da yake gabanta ya fi karfin ajiye faduwar shi a ranta, tana shiga wurin taron baki daya ta manta da wani, suna zaune a wurin har aka tashi, sannan suka nufi dakin su. Suka dauki kayan su, suna fitowa bakin get suka hadu da Ya Muhsin dan Yayan Baban Husnah, abin dariya a madadin ta shiga gaban motar, sai ta koma tana rab'e rab'e kamar ba zata shiga ba, su kuwa suka wuce baya suna mata dariya, tun sanya shiga gaban motar ta kifa kanta a saman cinyar ta. Sai dariya yake yana mamakin kunyar Husnah haka ya ja su, har gidan su Husnah suka wuni zuwa yamma aka wuce da Rahilah gidan uban goyonta a kofar gidan aka sauke ta tana d'aga musu hannu. Suna tafiya ta shiga cikin gidan. Yayan Babanta ta gani da manyan baki, bata san su ba. A dan tsorace ta gaida su. Ya fatota yayi da hannun shi. Ya nuna mata wani mutum. "Wannan dan uwan mamanki ne. Sun zo daga Yola ne ganin ki" wato da ta fashe da wani irin kuka, ta rungume shi, shi kasan kasa rike kukan a'a yayi yana shafa bayan ta, kuka take tana girgiza kai. Shafa bayan ta ya shiga yi. "Alhaji Zailani zan tafi da ita Yola." Cikin yar taburman kunya ya ce. "Allah sarki idan ka tafi da ita kar kace zaka rike min 'Ya da ita nake tuna dan uwana da matar sa." "Ba zamu rike ta ba, zan dawo da ita idan Hutu ya kare." "Ai shi kenan " ya fada yana kallon yadda take kara rike hannun Kawunta. Cikin gidan ya ce ta shiga gobe zai zo daukar ta. Dakyar ta amince. "Allah sarki da alamu tana kewan iyayen ta ne." "Eh barista. Alhaji zamu tafi sai goben in sha Allah." Haka suka yi sallama. Tana shiga cikin gidan, Mama ta dauke kai kamar bata ganta ba, bata kula ta ba ta shiga dakin su ta fara gyaran dakin tana mita a ranta. Har ta gama ta share dakin sannan ta fito ta ja ruwa a rijiya ta wuce wanka, tana fitowa. Yayan Babanta yasa aka kira ta. Sannan ya mika mata kayan da dan uwan Mamanta ya kawo mata, ta karba tana alamar godiya. Ta bar wurin dakin su ta koma ta fara bude kayan a dakin su. Tasan bata da rabon abincin rana, kuma bata saka kanta ba. Tsarabar da aka kawo mata shi ta ci ta koshi sannan ta wuce ban daki tayi alola domin lokacin la'asar yayi. *** Abdul Hakim, sai wurin karfe biyar na yamma ya bude idanun shi, ganin shi kwance a saman gadon asibiti. Yasa shi mikewa zubur, yana kallon Mahaifiyar shi da take zaune tana duba jarida. "Hajiya Ina yarinyar da ta zo kaina?" Ajiye jaridar tayi tana kallon shi kafin ta ce mishi. "Babu wata yarinya, tashi kayi lokacin sallah ya wuce maka" "Hajiya yarinyar" "ka wuce kayi sallah, bana son magana. Sai da nace kar ku tafi tare ina son ganinka shi ne ka bi shi. Yanzu kuma ka je ka kwaso aljanu zaka saka ni gaba" ta fada cikin matsanancin masifa, bai kula ta ba sai ma wucewa ban dakin da yayi, ya dauro alola. Sallah azhar da la'asar ya sauke tare da fatan Allah yasa ba aljana ba ce, "sai ka tashi ka ci abinci." Yasan idan ya ce ya koshi jidali ce, don Allah ya tashi ya karbi abincin da ta zuba mishi, har ya fara cin abincin ta wurgo mishi wata mahaukaciyar tambayar da ta sanya shi kwarewa. "Wai kai da matar ka waye bai da lafiyar haihuwa ne?" Tari ya fara, mika mishi ruwa tayi. "Eh jika nake so kai ne baka da lafiyar haihuwa ko ita ce, idan kai ne sai a sallame ta idan kuma ita ce sai ka kara aure wannan shi ne gaskiyar maganar " shiru yayi yana kallon kasa. "Hajiya lafiyar mu lau " "ungo naka nace Abdulhakim! Sai na zabga maka Mari" shi dai bai ce mata kome ba, ta cigaba da masifa" inda na tabbatar kai ne sai kaci kaniyar ka, domin ba zan yar da na zauna ina kallon ka a idanun kamar me lafiya amma a bad'ili kafin kowa matsala ba" hàdiye yawu yayi yana kallon abincin sa. Wacce irin tsana Hajiya take mishi haka? A hankali ya ajiye plat din ta daka mishi tsawa. "Dauka ka cinye min ko ranka ya b'aci" kamar yaro karami haka ya dauki abincin yayi ta cusawa kamar zai yi amai, shigowan Dr Sharif da Aunty Faridah yasa shi sake ajiyar zuciya yana kallon su." Cinye min ko na sab'a maka" "idan ya koshi a kyale shi mana" inji Dr Sharif yana amsar plat din. "Yaya ya jikinka?" Inji Aunty Fareedah. "Da sauki sosai Aunty Mom." Mikewa Hajiya tayi tana tsaki." Zan tafi sai a baka nono" babu wanda ya ce cikanki har ta fita. "Abba akwai yarinyar da tazo." "Auya sunanta Sa'adatu Aminu Fulani." Wani irin abu yaji tun daga tafin kafar shi har tsakiyar kan sa. Murmushi yayi ya ce. "Abba tana cikin masu gama makarantar ne?" Murmushi shima yayi yana girgiza kai. " Yar aji hudu ce." Murmushi ya kuma, shi daya sai murmushi yake ya d'ago zai magana Aunty Fareedah ta ce. "The charm prince met cendirellah." Wani irin blush tayi yana ji wani irin kunya. "And kana sonta" wani irin yanayi yake ji na wanda bai san mai zai ce ba. "Fiye da so!" Dafe kirjin shi yayi daidai bugun zuciyar shi ya ce. "Tun da na hango ta daga can nesa naji zuciyata ta daina bugawa," bai san ya aka yi yake sake magana haka ba, sai dai yasan sakon daga zuciyar shi ce, ya kasa control din kan sa. Su kansu dariya suke mishi domin ya samu abin da yake so. "Amma ka sani kurma ce." Murmushi yayi ya ce. "Abba nima bani da lafiya, gara it kurma ce ni fa? Rayuwata tana tsakanin mutuwa da rayuwa, gara ita zata iya rayuwa mai tsawo da farin cikin, nifa? Babu tabbacin zan kai har haka. Domin kullum da ciwon karfen nake kwana." Jikin su yayi mugun sanyi sosai. ---- Tunda Husnah suka sauke ta shiga cikin gidan, ganin Inna Larai yasa ta daka tsalle ta rungume ta. Suna dariya yayin da Rabi da Harirah suka rufa mata aka shiga farin ciki. Tambayar su tai me ya kawo su? "Baffa bai da lafiya yana Asibitin koyarwa na Udut. "me yasa me shi?" Watsar da hannu suka yi suna fada mata basu sani ba. Dakin Aunty Ummy ta shiga tana tambayar ta, me yasa mu Baffa. *** Kwara. Idan Allah ya tashi jarabtar ka, babu tsumi babu dabara, haka ne ya faru domin baki daya kowa yana mai da hankalin shi gidan rasuwar, yayinda aka bar Ummy Aymana da Latifah a asibitin wurin Ummi wacce bata san inda kanta. Haka suka cigaba da da zama, har zuwa dare da Ummin ta farka. Fita Ummy Aymana tayi ta kira likita. Koda likitan yazo ya gama dubata. Sannan ta mata wani allura ya ce musu. "Zata farka jikin da sauki gobe, amma don Allah kar a d'aga mata hankali ko abin da zai d'aga mata hankalin. " Gyad'a mishi kai suka yi, har ya fita babu wanda ya iya magana, sai can dare Abuturab ya kira su, ya tambayi jikinta suka ce da sauki. Washi gari. Da asuba ta farka tana farkawa kuwa ta tubure a sallame ta, babu yadda suka iya dole suka sallame ta, tana isowa jikinta ya dauki rawa, tabbas akwai wani bakon al'amari da zai faru, idan har lissafin ta daidai ne, kasa cigaba da ta kawa tayi tana kallon yan zaman makokin, kai tsaye ta wuce falon Sultan. "Ina Umar Saraki?" "Badi'atul me yasa zaki ce a sallame ki?" "Ina Umar Saraki?" "Ya ce kin kira shi, kin ga inda yake zaune kika kira shi ko ?" Da wani irin azama ta fito da gudu daidai shigowar Ambulance cikin gidan, cak ta tsaya tana kallon motar, wani irin rawa jikinta ya dauka. "Ina Abuturab?" Ta tambaye su jikinta yana sake daukar wani irin rawa. Kamar makauniya haka take bin motar tana shafa shi. "Sarakina yana nan, me yasa kuka bar shi ya fita?" Wasu mutane biyu suka fito daga motar bayan sun bude motar, baki daya suka yi bayan motar, Umar saraki ne a kwance kafar shi sanye da takalmin shi kafa daya, babu kafa ɗaya. Rufe baki Sultan yayi, bai tab'a ganin tashin hankali irin na yau ba, a hankali ya taka har gaban gawar ya bude yana kallon Umar saraki kwance, gaban goshinsa ya lutsa, jini yana fita ta hancinsa da kunnen shi. "Ku saka hannu anan." "Me yasa mishi a ina kuka same shi ina motar shi?" "Muma kiran mu aka yi, yayi hatsari a yadda aka gaya mana, motar shi ce tayi faci, shi ne ya fito zai sake taya. Wata motar daukar yashi ta zo da gudu ta make shi." "Sun kashe min d'a na biyu." "Badi'atul wannan wani irin zance ne, Abuturab zo ka taimaka mana a wuce da shi." "A'ah a'ah bar shi na boye shi kar su same shi, shima iya shi ya rage min " ta riko hannun Abuturab suka wuce can cikin part dinta, yadda zaka tabbatar da a gigice take, baki daya ta fita hayacinta. Kokarin niman maboya take tana son saka shi. Bude wardrobe tayi tana kokarin shiga tana cewa. "Zoka boya babu me ganinka " rungumar ta yayi yana kuka, "A'a Ummi, kij manta ko a cikin ki kika mai dani mutuwa zata bibiye ni? Ummi Ina yarda da kaddaranki yake? Ina imaninki yake? Yaushe zaki yi ta boya saboda mutanen da baki sani ba? Kar ki manta basu cutar da kowa ba, kema baki cutar da kowa ba, Ummi wallahi bana raba daya biyu su din bayin Allah ne, kuma kowannen su bana cire tsammanin yan aljanna ne, don Allah ki daina kokarin gudun matsalar ki." "Dole ka bar garin nan, ka tafi can can ka tafi su nime ka su rasa, ka nisanci masarautar don Allah." Tayi kamar zata durkusa mishi , rike ta yayi yana kallon yadda ta firgice. "Zauna " ta fada mishi, ba musu ya zauna yana kallon yadda take kokarin ganin ya zauna domin kar wani abu ya same shi. "nasan Ummina jarumar Uwa ce, wacce take tsayawa domin kare maslahar ta, idan har Ummina ta juya a guje waye zai tallafi rayuwar Sultan? Wannan yakin ba iya ke daya bace, har da Sultan ne karki manta suma Yaran sa ne waye zai rarrashe shi a rashin da yayi na manyan yaran shi a cikin kwanank tsakani? Idan har Ummin da na sani ce tow wallahi ba zata zauna domin wasu da manufarsu ba, ku barni na tsaya akan gawar dan uwana, kin ga sai buga mana kofar ake. Please Ummina nasan ke me hakuri ce da yarda da duk abin da Allah ya ƙaddara miki " "tow naji kar ka kula kowa." "Na yarda" dakyar ya fita ta bar ta da yan uwansa, har zai sauka Zakiyyah ta kwaila mishi kira, dukkan su uku haka suka tawo da gudu suka rungume shi, wani irin nauyi yaji ya karu mishi, kamar ya cire zuciyar shi ya huta. Dole yayi aure ko don taya Ummi ɗaukar nauyin yaran yayun shi. "Kun rike ni, kar na kai gawar Saraki kenan?" "Tsoro muke ji kar wani abu ya same ka" murmushi yayi sannan ya ce musu. "Idan na mutu gaku nan " ya fada yana janyewa daga jikin su, yayi tafiyar shi domin baya son suga karaya da hawayen da yake cikin idanun shi, kusan tunda ya tafi falon Sultan gawar na ajiye babu wanda ya tab'a, shi ya isa ya dauki Almakashi ya yanke rigar, yana cire kayan hawaye na zuba daga idanun shi. Sai kallon shi duk dattawan suke. Shi kan Sultan yaƙe yadda hawayen bai hana shi kome ba, a falon aka wanke Umar saraki, aka shirya shi, Abdulrashid da Abdulkarim da yazo suka fara gyare-gyaren falon, a lokacin aka kira Aneesah wacce ta kasa ki kuka sai ajiyar zuciya, "Abuturab kashe min mijina suka yi, wallahi kashe shi aka yi. Maina ma kashe shi suka yi, ka binciko duk me hannu a cikin kisan su ka hukunta shi, duk wanda ya kashe su shi ya kashe Mansurah dole a hukunta su." Abu daya ne ciwon mutuwar mijinta ne yasa take surutu. Koda aka kawo Ummi sai idanu bata ko iya magana abin tausayi. Sultanate kan tsabar tashin hankali sumarta uku, tana kuka tana cewa don Allah mutuwa me yasa bata dauke ta ba, ta bar Yaran da babu ruwan. Haka aka tafi aka sallaci gawar. Bayan an kai shi aka dawo sabon zaman makoki aka cigaba da yi, duk da a ranar Maina ya cika kwana uku, ana sallah la'asar aka mishi Addu'a. Haka kwanaki suka tafi, har aka Addu'oin bakwai maina da Addu'ar ukun Saraki a rana guda, daga nan aka watse. Bayan sati biyu. Ummi ta saka Abuturab ya bar ƙasan, ya koma Ingila da Baban Latifah zai koma suka koma, abin tausayi ranar da ya koma yayi kuka kamar ta cire zuciyar shi ya huta. Domin kuwa yadda kome yake dawowa akan idanun shi kamar yanzu abin yake faru. Ya manta da Sa'ade da farko yayi alƙawarin idan kome ya lafa wato bayan rasuwar Maina zai je yaga yadda take, sai dai Mutuwar Saraki yasa baki daya ya manta da ita. Yanzu gani Nigeria yake like hell. Ya tsani Nigeria baya jin zai kuma taka kafar shi kasar. *** Sokoto. A cikin sati biyu Abdulhakim ya hana kansa sakat akan Sa'ade sai damun mahaifin sa yake yaje a yi Maganar da manyan don Allah. Uban yace mishi auren dole yake nufi a mata, ya nime soyayyar Sa'adatu Aminu Fulani, ya shirya tsaf zai tafi niman ta, amma ta ina zai fara niman ta.. *intermission* Abuturab ya tsani Nijeriya, Abdulhakim yana can yana haukar niman soyayyar abar kaunar shi, ita kanta bata san halin da ake ciki. Yawwa yanzu zan ja zaren yadda labarin zai bada citta.... Ku tanadi tissue paper 🤧 [08/06, 9:18 am] usmanlauratu71: 31... Kawun Rahilah ya dauke ta, suka tafi Yola. Tun daga Sokoto suka dauki mikati babu bata lokaci. Kallon hanya take tana jin nutsuwa a ranta, babu abin da yafi dangin Uwa dadi, haka suka bar sokoton a fatar ta ma, ta tafi kenan amma idan ta tuna bata cewa su Husnah da Sa'ade goodbye ba, sai ta ji kamar bata kyauta ba. Kuma bata cancanci tafiya babu sallama ba, haka yasa ta kwantar da kai. Tana lumshe idanun ta, tana kewan kawayen ta babu laifi. Musamman Sa'ade don haka ta kwantar da kai tana jin barci yana fisgar ta, *** Kwara A can kuwa ba karamin ciwo Sultanah Badi'atul Noor tayi ba, domin wallahi mutuwar Yara biyu a kwanaki kusan daya yasa ta ta gigita, sai dai dake akwai Yaranta a jikinta yasa ta fara samun sauki, domin kuwa suna ƙoƙarin gano abin da zai sakata farin ciki. Part din Sultanate. Kallon Waziri Dawood tayi kamar ta rufe shi da duka, amma babu yadda ta iya. "Sultanate, mutuwar maina a rahotannin lafiyar shi an tabbatar da guba aka yi ta bashi har ya rasu." Wani birkitacciyar kallo ta mishi kafin tayi kwafa tana faɗin. "Kuma sai aka ce maka nice na bashi gubar ya ci kenan?" Girgiza mata kayi yayi yana murmushi. "Kar ki manta ni lauya ne kuma manazarci akan siyasar masarautar nan, bana zargin hannun ki a cikin kashe su sai dai akwai abu da kika sani akan mutuwar su." Kallon shi take tana mamakin abin da yake fitowa a bakin shi. "Kana nufin ina da wani abun da nake boyewa kenan?" Ta kuma wurga mishi tambaya. "Ko daya tambayata biyu ne, bayan su bana jin zan kuma tambayar ki, wannan gubar ba wata guba bace idan nayi duba da irin gubar da aka kashe Abdulsamad da shi" kamar wacce aka watsawa ruwan sanyi haka jikinta ya kama kerma bakinta yana rawa ta ce. "Tow ni ina ruwa na da wata guba da aka yi amfani da ita" "Me yasa aka kashe jikan gajiya? Me ya faru a daren kashe Mansurah ai duk sun samu alaka dake, Sultanate ranar da Maina zai rasu kin kira shi a waya kika ce mishi ya kula da rayuwar shi. Ranar da Saraki zai mutu kin kira shi kika ce ya kula da kansa, sannan kin gayawa Abuturab shima ya kula da kansa shin takun sakar da kuke da Badi'atul ne yasa kike bin Yaranta da su kula da rayuwar su?" Zuba mishi idanu tayi har ga Allah ba zata iya karban laifinta ba, domin abin kunya ce a ce tana uwar sarki guda ta amshi laifin da tasan tana da alaƙa da su, dauke kai tayi sannan ta ce. "Kana wasa da kujeran ia ne?" "Yo me zanyi da wannan kujeran ni wacce Abdulrahman yake kai nake so" gyara zama tayi tana wani munafikin murmushi ta ce mishi. "Wannan kujeran kare shi nake da lafiyata da rayuwata da kome, duk wanda ya nemi shiga tsakanin Abdulrahman da kujeran nan sai duniya ta ji mu da shi." Tana fadar haka ta mike ta bar falon domin ba zata kuma kula shi ba, ranta babu dad'i. Mikewa tayi tana faɗin. "Ga takardun nan ki tuna, duk lokacin da uwar da ta gaza kuka saboda shakuwa da Yayanta tafito farauta. Zata farauci kowa ne kamar yadda zaki ke farautar abin da zai ci, kiyi fatar mutiwa kafin ranar mutiwa tayi." Yana fadar haka ya juya ya fice, a bakin kofar falon suka hadu da su Abdulrashid da Abdulkarim. "Baba waziri yadda kake kokarin gano abin da yake faruwa me yasa baka gano mutuwar mahaifin mu ba?" Juyawa yayi yana kallon su. Kafin ya ce musu, "zaku iya daukar lauya ya muku bincike ni kuma zan baku documents akan binciken lafiyar mahaifin ku" "mun gode sosai" inji Abdulkarim. "Lauya ka kula da rayuwar ka, domin kana shirin saka kanka a cikin hatsari, wannan al'amarin na gidan sarauta kamar guguwar sunami ce, idan ta tashi babu wanda zai tsira a cikin wannan yanayin. " "Kai dai baka da hankali kullum sai ka kwafsa Baba waziri jeka kaji." Daga nan wucewa bangaren Badi'atul Noor ya shiga falonta tana kwance. "Assalamu alaikum " tashi zaune tayi suna amsa sallamar shi. "kina kwance ne? Waye yace ki gwadawa makiya kin razana? Kin bani mamaki tuf kamar ba Yar Alkali Abubakar Aalim ba? Wallahi ina baki shawara maza tashi ki daura d'amarar yaƙi, zaki rayu ne domin Jikokin da Aliyu, idan ta kama ki kashe ko ki b'atar domin ki rayu da Yaranki dole kiyi, ai suma suna haka ne domin wancan kujeran da shashashan Mijinki yake kai, daga babu jinya sai tsagwaron fansa, and zan baki wata karamar shawara." Yayi maganar da bana iya ji sai ita, zaro idanu tayi tana kallon shi bakin shi yana rawa, ya ajiye mata wani karamin gidan memory, ga shi idan kin samu damar fahimtar kanki akwai wasu number ki kira sako zai iso miki. Ki sani zaki yi ne don Abuturab, zan tafi" gyada mishi kai tayi tana juya gidan memory din sannan ya fita. Yana fita motar shi ya shiga, yana fita bakin masarautar ya tsaya Sakamakon wucewa Mai girma gwamna da yazo gaisuwar shi, dake akwai motoci dayawa, tsayawa yayi can motar gwamna tana wucewa aka ga motar Baba waziri ta kama da wuta. Haka ya kuma gigita Badi'atul Noor, domin labarin ya iso har mai girma gwamna sai da suka fito, mutuwar Babban mutum lauya ne matsayin SAN ya mutu Allah sarki. *** Asibitin da aka kwantar da Malam Aminu, kullum sai Sa'ade tayi amma bawan nan cewa yake ba sa'ade shi bace, wannan wata yarinya ce, sa'aden shi ya sayar da ita da hannun shi. Kullum zasu kai abinci da Aunty Ummy, wanda karshe dai wata ran da kanta take kaiwa ba sai an raka ta ba, yau ma da wuri ta shirya dauke da basket xin abinci tana tafiya har ta kusan shiga bakin hanya, sai ta samu abin hawa. Abdul Hakim da shigowar shi kenan unguwar yazo wurin wani abokin shi, ya hango ta tana lissafi da hannunta, ai babu shiri ya karya kan motar ya bi me tricycle din, har kofar asibiti inda me tricycle din ya tsaya, ta biya kudin. Murmushi yake she too young asalin karama ce, amma zaa yi doguwar mace, tana da kayan albarka na dai-dai shekarun ta, don ma hijab ta saka sai dai da alamu irin siririya ce, wacce idan ta samu dama zata zama katuwa haka yasa shi bin ta da mota har cikin asibitin, tana tafiya a hankali kamar tana tausayin kasar. Har ta isa inda Ward na maza yake, sai dai masu tsaron kofar sun hanata shiga, komawa gefe tayi tana jiran wanda zai mata sanadin ta shiga, yana ganin ta ya sake murmushi wannan ya bashi damar kusantarta. Yana zuwa ya gaishe su. "Officer ku barta ta shiga mana" "Yallabai ba lokacin ziyara ba ne." "Eh tow kuna ganin ba zata samu shiga ba kenan sai na bada na shan ruwa" kallon juna suka yi, "yallabai kasan dake aikin." Takowa yayi ya saka hannu a cikin aljuhun shi ya zaro yan dari biyar biyar ya mika musu, kafin su karba sun bude mata kofa. Kallonta yayi tana kallon su, yace. "Shiga" da kallon bakin shi ta fahimci abin da yake nufi, gyada kai tayi. Ta shiga a hankali ta fara nazarin a ina ta ga fuskar shi. Da sauri ta juya ai bata san lokacin da tayi wani irin ja da baya kamar zata fadi ba, yana tsaye a bayan ta. "Na baki tsoro" da sauri ta yi cikin ward din, tana tafiya yana bin bayan ta har suka shiga inda Malam Aminu yake. A tunanin ta wani yazo dubawa, sai dai ganin shi tayi yana binta har inda Baffan ta yake. Kamar ta zunduma ihu. Murmushi sakar mata, ya kalli Inna Larai ya ce mata. "Sannu Baaba yame jikin?" "Da sauki" ganin yayi ward din an cika hayaniya kasa kasa. Kallon Sa'ade yayi tayi tsuru-tsuru ya cewa Inna Larai. "Tun yaushe kuke nan?" "Sati biyu kenan" girgiza kai yayi ya jima sosai kafin ya saka musu kudi ya dan saci kallon Sa'ade yaga yadda ta rude. "Toh Baaba Allah ya bashi lafiya" "Amin Ya Allah, mun gode da dawainiya." Ba kome. Fita zai yi Inna Larai ta taɓa ta. "Ki tafi ki same shi" girgiza kai tayi tana gaya mata da hannu. "Ban san shi ba" "a'a ke ya biyo ki je ki sallame shi." Kamar zata fashe da kuka haka ta fito ta same shi a waje hannun shi harde hannun shi a kirji yana kallon ta, yadda ta dauke kai zai tabbatar maka da yar kurma bata maraba da shi, hana ya gama tsayuwar shi, ya matso kusa da Ita, yana leka fuskar ta yaga yadda ta lumshe idanun ta, ko ba a maka bayani ba kasan amsar shi ne bata kaunar ganin shi. Shi kan ma abin mamaki yake ba shi. Haka ya karaci tsayuwar shi ya tafi. Tana daina jin kamshin sa ta bude idanu ta wuce. Karfin hali irin na shi sai ga shi yasa an sauya musu daki, daga ward zuwa aminety. Abun ya bawa su Inna Larai da Zakaria, haka suka koma suna mamakin wannan sauyin karshe dai zuwa yayi bincike anan ya ji ai wani ne ya biya kome da za a bukata, da ya bukaci jin waye ne? Suka ce basu sani ba, daga sama ne don haka ya hakura, ya dawo. Shi kuwa Abdul Hakim bibiyar motsin Sa'ade, da inda take har inda yayunta suke aiki da garin su, yana samu labarin yafi kowa farincikin. Sai dai wani abu daya da ya kasa fahimta shi ne ita bata kula shi duk yadda yaso ya mata magana baya gabanta. Haka yayi ta binciken har Maikulki ya tafi dan jaraba, anan ya ji labarin Aliyu Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, ran shi ya matukar b'aci taya haka ya kasance domin a yadda ya ji labarin, yasa shi ba zai tab'a give up ba, domin yaji labarin da yake jin ko mutuwa zai yi ba zai barta ba, kuma wanda ya gaya mishi ba masa karya ba, domin Nazifi ne dan mai gari ne, shima ya samu ganin shi ne ta sanadin wani ma'aikancin kamfanin simintin sune, wanda shi dan garin Binji ne ya gaya mishi yasa Nazifi yana aiki da ma'aikatan kudi, wanda Aliyu sulu gambari ne ya sama mishi aikin ta hanyar Sadeeq Shehu, shi ya gaya mishi gaskiyar da ba kowa ya sani ba. Amma malam Audu fir yaki sauraron abin da suka gaya mishi. *** Mutanen UK. Yadda ya mai da kome ba kome ba, zai baka tausayi. Fada yake da kan shi tare da yakin tsayawa da kafar shi, fafutuka yake ba dare ba rana, a duk lokacin da ya tuna irin mutuwar da yan uwansa suka yi, sai yaji kamar dole yayi yaki da kansa domin kamo masu laifin wanda yayi imani da Allah ba mutuwar Allah ba ce, akwai wani abu a kasa. Yau yana gama abin da yake ya fito a hankali. Idanun shi ne ya sauka akan Latifah. Gyara rike jakar yayi ya wuce wurin motar sa, hàdiye kwallar da ya cika idanun shi yayi yana kallon wurin da motar Maina take da, idan zasu tafi wurin aiki a tare suke tafiya a mota daya. "Hamma Auta" dan tsayawa yayi ya kalle ta. "Baka karya ba zaka tafi?" "Ina azumi ne" ya shiga motar zai rufe, da sauri ta riƙe kofar. "Me yasa kake share ni? Nayi maka laifin ne?" Murmushi yayi mata dimple point din shi guda uku suka latsa, biyu a kumatun sa, sai daya a habbar sa. "Baki min kome ba" yaja motar yayi gaba abin. "Anya bai san wani abu ba? Kai akwai abin da ya sani." Ta fada tana kallon motar shi har ya bar unguwar. A hanyar shi ta zuwa makaranta da aiki, idan aka tashi a makarantar sai ya wuce inda yake aikin part time, coffee shop ne, a wurin.... (Yau naga ikon Allah wata ta samu ana sonta sai wani jan guntun kwailarcinta take d'an hajiya Madam Daulah yafi karfin ki Malama 🤷🙅) 08130269641 [09/06, 9:09 am] usmanlauratu71: Yau ma yana tasowa wurin ya wuce, cire jacket din shi yayi, ya kai jakar shi da duk wani abu dakin da suke sauya kaya, ba iya coffee da tea ake ayi a wurin ba, babban wurin sayar da abinci ne, na wani bature, dakyar ya samu aikin shi yasa yake girmama aikin sosai. Suna dayawa masu aiki a wurin maza da mata, yanayin shi da fatar shi yasa yan mata suke turuwan zuwa wurin, ba iya yan mata ba duk manyan mutane ma suna zuwa, nutsuwa , Kamala, dattako, girmama kai, sanin darajar na gaba da shi, uwa Uba baya da wata dabi'ar banza, yana da hakuri don ba me yawan shiga abin da babu ruwan shi ba ne, haka yasa yan matan idan suka zo shan coffee sai sun ninka kudin shi, shi ba haka yake ba, asalima yafi karfin wannan kudin kawai yana haka ne don baya son zaman gida yana tunanin yan uwansa. Shi yasa ya fara aikin, yana gama canja kayan sa ya fito suka gaisa da abokan aikin sa, ya tsaya yana duba menu din wurin, yana kallon yadda mutane suka fara zuwa,. Murmushi yayi ya cigaba da aikin sa, kafin aka fara odar, ana zuwa yana kai musu. A cikin table din da zai kai na gaba, wata yar matashiya ta gani wacce zata kai shekaru shida zuwa sha bakwai, ita da Iyayenta da kannenta biyu. Tsaya yayi a kasan su yana rubutu. " Me kuke bukata?" Kallon shi Uban yarinyar yayi ya ce mishi. "Ba zamu yiwa bakar fata magana ba" yana fadar haka ya dauke kansa. Juyawa Abuturab yayi ya mikawa Mike Menu din. "yau bakin naku ne" sam bai ji haushin su ba, sana aja yawan samun masu wariyar launin fata, yana kallon su. Lokacin da Mike ya nufe su. "Sir me kuke bukata?" "Ku kori wancan bakar fatan a cikin ku, Yarana basu son shi." "A'a mu bama haka" mike ya gaya musu. "Tow zamu tafi" "ba damuwa zaku iya tafiya" ganin da gaske bai damu ba, ita Budurwar ce ta kalli Abuturab, lumshe idanunta tayi sannan ta bude ta kyafta sau uku uku. Kurawa juna idanu suka yi, ta kuma kyakfta mishi. Lumshe idanun shi yayi yana nazarin yadda take kifta mishi. Idan ya fahimci sako take tura mishi. budewa yayi yaga sun mike. Ta kuma kallon shi kamar zata yi kuka ta ware yatsu uku tana motsa mishi. Alamar "Please save me" dafe kansa yayi yanzu ta fahimci kurma ce. Da sauri ya nufe su yana faɗin. "Sir me kuke bukata kar ku tafi?" "Kai ne bama son gani" "ni" ya nuna kansa. "Yes kai ka bar shagon nan" ya kalli yarinyar ta kuma tura mishi sakon. "Ok na ji zan bar shagon, yayi muku?" Ya tambayesu, "eh yayi mana " haka ya fita, Manager dinsu ya kira ya gaya mishi, dake mutumin yana matukar son Abuturab a shagon take ya fito yaga yadda yarinyar take juyawa, dake shagon glass ne kana ganin na ciki na waje ma yana ganinka. "Sir ka fahimci haka kuwa?" A dame ya kalli wurin yarinyar. "eh na gane turab, amma ya zamu yi sai dai mu kira yan sanda" "ok" haka ya fada yana me niman yan sanda. Koda suka zo bayani suka musu sannan suka shiga, nufar table din suka yi, suna isa yarinyar ta mike dake sun musu bayanin kome, sun zo da wata jami'an yar sanda wacce take fahimtar sign language, tana tambayar yarinyar ta fara kuka tana gaya mata, sace ya suka yi suna gana mata azaba, haka yan sanda suka tattara su, suna yiwa Manager godiya, ya nuna musu Abuturab zasu yiws godiya. Ajiyar zuciya ya sauke bayan tafiyar yan sanda. "Sa'adatu!!" Wani irin ware idanu yayi, baki daya ya manta da ita, wayar shi ya Ciro a cikin aljuhunsa. Nazafi ya kira. "Hello" ya fada cikin sanyin murya. "Ranka shi dade, kana nan dama ?" "Ina nan Nazifi, Yasu Baba?" "Suna lafiya. Kwanakin baya Yarima Sadeeq yake gaya min an yi maka rasuwa? Ya hakuri Allah ya musu rahama." "Amin Ya Allah, na gode sosai Allah ya bada lada." Cizon bakin sa yayi kafin ya ce masa. "Ya take?" "Yallabai tana lafiya, sun kusan komawa ne ma?" "Yayi kyau." Sam Nazifi ya manta ya gaya masa Abdul sai kawai ya ce mishi. "Ka nimo min me acc din First bank zan turo maka sakonta, da list din abin da zaka saya mata. Idan ka kai mata kace mata ta jira ni." Daga haka ya suka yi sallama. Sauke numfashi yayi yana kallon wayar bayan kaman minti ashirin sai ga sakon ya shigo mishi, mai da wayar yayi ya cigaba da aikin sa, sai da lokacin tashin sa yayi, ya dauki kayan sa da key motar shi, yana me musu sallama. Wurin motar sa ya nufa ya tsaya zai shiga tace mishi. "Halftime" juyawa yayi yana kallonta. "Sarah" ya furta a hankali ya bude motar zai shiga ta zaga zata shiga, zama tayi tana kallon shi. "Sakonin da na turo baka yi reply ba, na kira ka severally time baka yi picking ba, wai na tambaye ka, wacce mace ce ta hanaka kula ni?" Bai kula ta ba suka shiga tafiya. "Ai san gidan shi yasa da na tambayi wacce mayyar ta gaya min kana halftime Job biyoka. Da ace na samu wata mace tana kula ka, sai na kashe shegiya." Har suka isa gida abu daya take fada, Latifah tana tsaye suka dawo. Ranta yayi mugun b'aci, amma sai ta danne kamar babu wani abin da ya b'ata mata rai. Zuwa tayi ya tsaya yana fitowa ta amshi jakar shi. Shi kuwa ko ta kan su bai bi ba, ya shiga falo da sallama, Iyayen Latifah ya samu da Hajiya Suhailah. A mutunce suka gaisa, sannan ya wuce ya bar musu falon,, a kofar part din ya samu Latifah da Sarah sai gayawa Juna magana suke, mika hannu yayi Latifah ta mika mishi jakar shi, yana bude kofar da card dinsa ya shiga bai basu damar shiga ba. dakin sa ya wuce ys ajiye jakar sa, ya nufi kitchen ya daura abinci ya koma ban daki yayi wanka sannan ya fito ya shimfida abin sallah, ya sauke la'asar din kansa, yana azkar ya fito ya nufi kitchen ya haɗa girkin sa, bai ma damu da cin abinci mai nauyi ba, kunun tsamiya ya dama, ya sha da brown sugar. Yana gamawa, ya fito da keken shi ya fita. Suna kallon sa, can inda ake train na kwallon kafa ya tafi yana me train. *Da na same ka da wata mace sai na kashe ta* cigaba yayi da buga kwallon. Juya maganar yake yana karawa har dare ya fara rufawa. Ya dauki keken shi ya komo gida. A bakin get suka hadu da Latifah zata fita aiki. "Ka dawo?" Ta fada tana kallon shi. Kiranta yayi da hannu, da sauri ta karaso wurin shi. Kafa keken yayi ya nufe ta, sai da ya ciro hanky a cikin aljuhun rigar shi, ya fara gogo mata fuskar ta. "Are you okay?" Hawaye ne sharrr suka zubo mishi. "Babu kome" "gaya min me aka miki?" Cikin tsoron abin da zai faru tace babu. "Gaya min nace" ya daka mata tsawa, "wai Sultanate ce ta turo Sarah da Mamanta su zo ku daidaita kanku?" Kura mata idanu yayi, kafin ya ce mata. "kina sona ne?" Wasu sababbin hawaye ne suka shiga suka shiga zuba mata. "Hmmm, but ina da wacce nake kauna sama da Mansurah" ya fada yana kallon ta. "Ina kaunar Sa'addah, and babu me min dole. Bar kuka ba zan auri Sarah ba, bayan ga ki a gabana" "Ni baka sona ne?" Ta tambaye shi cikin kuka sosai. "Waye ya ce miki bana son ki, ina sonki mana so na yan uwantaka ba so na har abada ba " "meye banbancin?" Shi na yan uwankata Zumunci kawai zamu yi, shi na har abada, mutu kara ba. Sa'addah ba sonta nake ba, domin so zai iya saka na hada mata reval." "Mansurah da?" "Ita son zumunci ce, koda na aure ta naga Sa'addah tow ba zan iya adalci a kanta ba, ina kaunar Sa'addah " sake baki tayi tana kallon shi. "Me ye banbancin so da kauna?" "Shiga mota" shiga tayi, ya ja ta suna tafiya yana jin kamar tana tsakurin shi. Nan ya shiga gaya mata banbancin so da kauna, da yadda yake jin sa'addah har suka isa asibiti. Daure fuskar shi yayi yana kallon ta. "ki kula da kan ki" tana fita ya nufi gidan. A bakin kofar gidan ya same Sarah. Fita yayi a motar, ya riko hannunta suka nufi cikin gidan, yana shiga falon ta wurga ta saman kujeran. "Kawu me ya faru Latifah ta fita da kuka?" "Shi ne zaka riko ni ha..?" "Keep quiet" ya daka mata tsawa, sai da idanun shi suka yo waje, kamar ta sake fitsari a jikinta, wani bala'in kwarjini ya mata, juyawa yayi ya kafe su da idanu. "Sultanate ce ta aiko su wai tazo ku daidaita kanku?" "Hajiya Suhailah kike? Ki tafi ko gaya mata ina da wacce nake so, a cikin gidan nan take don haka ba zan auri wannan mara tarbiyyar ba, maza kafin na fito na ji labarin kun bar ingila domin tun ina Aliyu Abuturab, kafin na juye izuwa Aliyu Asad. Ku bar gidan nan." Har ya mike ya ce. "fushina da fusatatta zata ninku ne idan nayi ido da wancan mahaukaciyar Yarki " babu wanda ya samu zarafin magana sai dai idanu kawai. Yana barin falon Sarah ta fashe da kuka. Takaici ne ya rufe uwar ta mike." lallai Aliyu bai sanni ba " "ko ya sanki babu abin da zaki iya mishi.kuje kafin ya kuma ganin ku " daga haka suka mike, ranar a hotel suka kwana. Washi gari suka bar kasar. Yana barci kasancewar bai da morning class, ya kwanta yayi ta barci. Kiran Ummin su ya sa shi bude idanu. "Ummina?" "Naji sakon ka, idan har Sultan ya kira ka, ka amshi auren Latifah. Amma ka bar london " "Ummi na, na fada mata gaskiya ina da wacce nake kauna. Na fadi haka ne domin su kyale ni " Murmushi tayi tana faɗin. "Kai mutum ne mai daraja, koda kana da wacce kake kauna, ina son ka amshe ta, tunda ka fada kana sonta." "Saboda me yasa Ummina?" "Saboda kai ne Yarima me jiran gado, idan ka fadi magana ana nufin daga zuciyar ka ta fito ba daga bakinka ba, ka karbi auren " "taya zan zauna da macen da bana sonta." "Idan ka aureta ka zuba mata idanu, mara kunya." "Shi kenan zan yi yadda kika ce." "Kai bana son shirme." Ta fada. Duk yadda yaso ya mata bayani kin kula shi tayi. Kallon wayar yayi ya ga sakon Nazifi, mikewa yayi ya nufi wardrobe din sa, ya dauki rigar shi ya saka, sannan ya bude wani kwali ya dauki kuɗi, ya fita da shi. Bankin first bank ya nufa a can ya tura kudin sannan ya wuce coffee shop din su, anan ya karya, suna mishi tsiya. *** Mayye ko nace dan anace, yana can ya nace karfi da yaji ya cusa kansa cikin familyn Sa'ade, babu abin da yake bashi mamaki kamar yadda tsakanin ta da Allah take nuna mishi kiyayya, bata kaunar shi. Yayi iya kokarin sa amma baki daya taki kula shi. Yau da aka sallame Baffan su, har gida ya kawo su. Lokacin da aka fita zuwa cikin gidan Zakaria. Riko hannunta yayi ta juya a fisace kamar zata mare shi. Mika mata takardan hannunsa yayi. Amsa tayi ta bude. "Ina sonki!" Kallon biron da yake jikin sa tayi, ta rubuta mishi. "Bana sonka ina da wanda nake jira" tab'e baki yayi sannan ya d'aga kafad'ar shi alamar oho. Bata bi ta kansa ba, ta wuce cikin gidan. Hutawa Baffan su yayi aka kawo mota za a mai da shi Maikulki dan iya ya shiga gaba shima zasu tafi tare. Abin haushi sai wani jida shi Baffanta yake, haka suka isa har Maikulki, tana bayan motar da Baffa Yusuf da shi suna gaba, har garin suka isa. Daga nan gidan mai gari ya wuce. Bayan ya nime iso aka kai shi. "Sannu yaro daga ina kake?" "Daga sokoto, Baba nazo niman izinin ka shiga min gaba a bani auren Sa'adatu ne." Tashi zaune mai gari yayi, ya ce mishi. "Kaga Yaro na gaya maka gaskiya ko na Barka?...... Idan na baku barka da Juma'a yau ba zan yi gobe Asabar ba, sai Sunday idan kuma ban baku ba, zan yi typing Asabar da Sunday. Zabi yana hannunku... 08130269641 [09/06, 6:09 pm] usmanlauratu71: 33.... "Gaya min koma mene ne zan iya dauka, amma ba zan iya daukar abin da zai shiga tsakanin soyayyata ba" Abdul ya fada, a hankali. "Yaro ia hakura da Sa'ade akwai nauyin wani akanta?" Mai gari ya faɗa mishi cikin sigar lallashi. "Baba Indai ha aure bane bana fatan na hakura da ita." "Akwai baikonta da wani!" "Baiko ba aure bane kuma ba zai saka na hakura da ita ba, Baba ni sonta nake kamar rai da kaddara, ina sonta daidai rayuwa da mutuwa, ka min adalci ka bani ita shine kawai abin da zaka min nayi alfahari da haka." "Kayi hakuri ba zan iya maka jagora ba, domin wallahi ina matukar jin kunyar haka. Ina jin kunyar na.maka jagora a baka aurenta domin akwai wanda yake sonta tun bata kai mace ba, yana sonta tun bata zama kome ba, tun babu kome na zama mace a jikin ta, ka bar mishi abin sa." Wani irin damuwa Abdul yaji da kunci, "Allah ya gani nafi shi bukatar ta, na fi shi son ta." "Baka fishi ba, domin ta ya zauna na tsawon wata guda, domin ta ya zama namu da har yau muke cin gajiyar ta. Don Allah kar ka yi wani abu mara kyau" "saura kwanaki nawa ya rage min da ba zan mallake ta ba." "A'a Yaro kai wani abu kake bi, da ace shima haka yabi da yanzu ba ka isa ka ce kana bibiyar ba, shi ita yake bukata duk wani abin yake domin ta yake yi na haɗaka da Allah ka bar ta " mikewa yayi yana faɗin. "Zan duba, amma ban yi alkawarin ba. Akan abin da nake so bana ji bana gani " daga haka ya fita gidan su Sa'aden ya koma, a zauren gidan ya samu Malam Aminu da abokinsa, dama yasan Malam Aminu son kudi domin yaji labarin shi, don haka ya bashi kyautar kudi masu yawan gaske. Sannan ya shiga ya gaida Inna Laminde ya mata sannu da jikin Malam Aminu, idanun shi yana kan Sa'ade da take faman share tiken dabobbin ta, wanda suka yi albarka. Nan ya shiga jan Inna Laminde da hira, tun bata sake ba har ta sake suka sha hira sannan ya tashi zai bar gidan idanun shi akan Sa'ade da take faman wanken kafarta saboda aikin da tayi. "Toh a gaida gida" Inna ta fada mishi domin hankalin sa yayi nisa. Jin muryan Inna yasa shi sosa kansa, sannan ya fita. Mikewa Inna tayi ta tab'a ta, "ki tafi ki raka shi mana" tura baki tayi tana dauke kanta. A ranta kuwa cewa tayi. 'Kamar ya tafi ya zauna mayye kawai' daga haka ta wuce abin ta. Ɗakin su Harirah ta shiga ta ja hijab ta saka, sannan ta shuri takalmi ta fito tana kallon shi yana jiranta, dauke kai tayi tana kallon wani wuri can. Haka ya gama tsayuwar shi, ya dauko pen da paper ya fara rubuta sakon shi. "Gimbiya ki daina wahalar da ruhina" ya ajiye mata a dakalin kofar gidan su da take jingine. "Ki saurari sakona" dauke kai tayi idan ta karanta yaga takardan take ta zubar. "Ina sonki" juyawa tayi ta zuba mishi idanu fess murmushi tayi ta mika mishi hannu taba takardan da biron. "Wallahi na rantse da Allah da girman sa bana sonka. Bana son ganinka ka fita a Rayuwata." Daga haka ta ajiye mishi takardan ta wuce. Dauka yayi yana kallon abin da ta fada, murmushi yayi yana shafa kansa, ya soke takardan. Ya shige motar sa. Sati daya na zagayowa sai gashi kamar dole, da ya tashi zuwa shatara na arzikn yayi musu, daga Inna har Sa'ade babu wanda abin ya burge shi asalima tsoro kayan ya basu domin basu tab'a ganin hauka irin na shi ba. Ido da Ido ta ce a mai da mishi kayan, ta kuma rubuta mishi cewa. "Ka tattara kayan ka, ka koma mu ba kwadayayyun mutane ba ne, mutuncin mu yafi karfin a saye shi, bar ganin bana magana kuma bana ji da kunne daya, ba yana nufin ban san me yake faruwa ba, don Allah na hada ka da Allah ka tafi da kayan ka bana bukata bana son ganin ka" ta ajiye mishi. Karantawa yayi yana kallon ta har bar wurin, tana tafiya ya nufi wurin Malam Aminu ya gaya mishi yadda suka yi, dake ya san kan duniya sai cewa yayi. "Ni ban ce zan mata dole ba, tunda tace bata sona ai shi kenan amma na mai da kayan nan ba dadi, gashi ba ni da lafiya ina fama da ciwon zuciya, don Allah baffa ka gaya mata bani da lafiya ta daina kina." Sokoto "Hajiya Barka da warhaka " gyara ƙwanciyarta tayi tana faɗin. "Yawwa Sophia ya kwana biyu, bana ganin Mijinki da fatan lafiya dai?" "Alhamdulillahi Hajiya, kawai nima wani abu ne ya kawo ni, ban sani na ba ko kin sani." Kallonta tayi na wani lokaci kafin ta ce mata. "Me kenan?" Mika mata takardan tayi, sai da ta juya sosai kafin ta tashi zaune, ta bude a hankali. "Bana sonka bana son ganinka a rayuwata" "laifin me ya Miki haka?" Domin ita a zatonta, ai Sophia ce. Girgiza kai tayi tana faɗin. "Bani ba ce, wata ce yake bi take wulakanta shi" ta fada rai a jagule, yadda zaka fahimci tana cikin damuwa sosai. "Yar uban waye da zata ce bata son shi? Waye ubanta da zata ce bata son ganin shi? Waye ya tsaya mata a kasar nan" yadda take tadda jijjiyar wuya zaka dauka Sa'ade tana gabanta ne. Sai bala'i take kamar zata ci kanta, ta kuma hana Sophia ta fita, haka suka zauna har dare kafin Abdul din ya dawo jiki a mace, duk da zuciyar shi yana ciwo, bai hana ya boye hakan ba, sai da ya shigo ya samu draman Hajiya, zama yayi a falon ta gyara zama. "Wata shegiya ce ta ce bata son ka?" Bude idanu yayi sosai, musamman da ta cilla mishi takardan. Dauka yayi yana kallon takardan sannan ya kalli Sophia da ta sauko daga sama. "Yarinyar da ta taimaka min ne makarantar da aka gayyaci Abba, wai tana da wanda take so ne shi yasa taki amsar tayin soyayya ta, sai dai nayi magana da mahaifinta ya kuma yi na'am da ni." "Matar da bata sonka zaka aura?" "Amma ai Hajiya wanda take so ya gudu ba asan yadda yake ba, ni kuma na shirya mahaifin ta ya ba ni damar" "wai tsaya a ina ne ma tukun?" " A garin Maikulki Binji local government" ya fada a hankali. Domin yasan abinda zai biyo baya. Dariya ya bata. "Yar talakawa yar kauye gaba da baya zaka dauko min " wani irin sarawa kansa yayi ya ce. "Ya Salam " "kaji da kyau ba zaka tab'a aurenta ba, gara ka nimo yar wani kusar gwamnatin gara da tace bata sonka ta rufewa kanta asiri da tace bata sonka domin ko ita ce Juliet ba zaka aure ta ba." "Hajiya gaskiya ina sonta " ya fada a hankali. "Shi kenan ayi muga ni." "Don Allah kar ki raba ni da abin da nake so." *** Kwara. A tsatsaye Sultan ya fara rashin lafiya, wanda yake ganin likita lokaci zuwa lokaci. Duk da ya boyewa kowa amma ya kasa boyewa Badi'atul Noor. Domin ita ce tafi dacewa ya gayawa, da farkon ciwon da ya fara, yana ganin likitan shi, ya bashi test kusan kala bakwai, bai yi wata wata ba, ya bawa Shatiman kwara, aka tafi a mishi. Lokacin da aka kawo sakomakon ya bashi tsoro, huhunsa ne ya fara kokarin kamuwa da irin muran da ya kashe Maina. Ba iya shi kadai ba, a gaban Badi'atul Noor aka fadi sakomakon. Kallon juna suka yi ta sake murmushi. "Ka gamsu kashe min Maina aka yi?" Lumshe idanun shi yayi domin Al'amarin ya fara bashi tsoro, amma sai ya dake. "Likita akwai Magani ne?" " Eh zamu fara maka aiki a kwashe ruwan cikin huhun, amma ina ganin sai ka bar kasar nan za ayi aikin a Canada ne. A can za a fi samun kulawa ga gashi a sayo magani." " Na gode" daga haka ya koma bangaren Badi'atul Noor baki daya ya zauna domin yaji a jikin shi a wurinta kawai yake safer, don sauran matan shakkar su yake zasu iya kashe shi ita kuwa bata isa kashe shi ba, tun zamanin farko ba ta kashe shi ba, sai yanzu. Abinci ta kawo mishi me saukin flavor don ko kayan yaji bata saka mishi ba. "Baka zargin wani yana blackmail dinka ba?" Girgiza kai yayi ya masifar bata tausayi. Dariya ta saka tana kallon shi. "Ashe haka kake tsoron mutuwa?" "Ba haka ba ne, ba san me nayi ake min haka ba, yarana duk babu magada na, Abuturab kuma an daura min zargin sa." "Like how?" Kallon ta yayi yana tararradin abin da zai fito bakin shi, yo dama ya lafiyar kura balle ta hauka ce. "Baka ce min kome ba, zargi kamar Ya? Dama zargin shi kuke?" Yadda ya kura mata idanu, itama kuma shi take kallo da sauri ta ja da baya ta ce mishi "A'a ko da wasa.... Allah ya kai mu Sunday in sha Allah gobe barcin safe zanyi da yan dagwai-dagwaina💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽 ololo oo buga wooooo.....08130269641 [11/06, 11:11 am] usmanlauratu71: 34... Wani irin ja da baya tayi tana watsa mishi wasu fusatattun kallo. "Me kake nufi?" "Kin ga saurare ni" "kar ka tab'a ni me kake nufi? Zargin shi kuke zai kashe yan uwansa? Kuna min dan Yaro karami irin sa zai kashe rai?" "Kin ga Sultanah" ya matso sosai kusa da ita, yana kallon ta, hannun shi ya kai da nufin ya rike ta, ta ce mishi. "Ko da wasa kar ka tab'a ni." "Naji amma lissafin a bayyana take, kome a shi ajiye yake, Badi'atul Noor! Abuturab yana barin garin nan aka samu gawar Mansurah, yana can aka kawo gawar Maina, yana nan." Wani irin mazari jikinta yake bata san lokacin da ta ce mishi. "Kenan shi a zuba maka wanda ka ci? Ko shi ya kashe SAN? Lallai lissafin ka baya ajiye inda ya da ce wallahi ka sake wannan al'amarin ya fita waje, zan ajiye girma da mutuntatta, zan mai da rigata da take ajiye domin kare jinin Yarana ba iya su ba, ga wanda yake karkashina ba zan yi asarar jinin shi ba. Kuma yanzu ba an jima ba fitar min a part yanzu nan" "Babu inda zani, wallahi yanzu ai na fahimci babu ruwansa tunda gashi ni ma kashe ni ake son yi don haka ki shafawa zuciyar ki ruwan sanyi malam" "taya bayan kiri-kiri gashi kuna zargin shi, na rantse da Allah wani abu ya fito sai na baku mamaki." Daga haka ta bar shi a wurin, baki daya sai yaƙe jin kamar yayi wani mara mara kyau. Haka ya kamata ya gaya mata cewa suna zargin shi? Sam bai dace ba. Abin da suka yi basu kyauta ba, koma meye zasu yi ai bai dace ya gaya mata ba, ko da yake ai haka shi ne daidai, ba da Abuturab din suke zargi ba Allah da ya tashi wanke su ya kawo al'amarin kansa. Gyara ƙwanciyar sa yayi domin babu wanda ya isa koran sa shi da gidan sa, Allah mata basu kyautawa kai da gidan ka ace ka fita ka bar musu fisabilillahi, idan ta gaji ta dauke shi ta watsa waje. Takaici ne ya Ishe ta bai ishe kowa ba, ta bar shi a yashe a falon ya ci bakin halinsa da munanan zarginsa domin babu adalci a cikin wannan al'amarin kuma zai sha mamaki domin sai ya bar mata part dinta, ya je can su bashi bindiga karewa guba, don haka ta kulle shi ta ajiye da ita yake wasan. Abin dariya yadda take fada baya wurin fa, amma faɗa take sosai kamar yana kafe a gaban ta. (🙄 Allah ya baki hakuri ki cikanki Ummi) haka ta gama masifar ta babu wanda ya san tana yi ta kuwa fito tana hararan inda yaƙe. Bata haushi ko wata ba ayi da rasuwar Yaranta ba, zai kawo mata wani zancen wai ana zargin Abuturab hala wanda aka saka mishi ma, abuturab din ne mutane kawai suna Judge dinka mutane da halin shi koda yake bata ga laifin sa ba, akwai wani munafiki a can.. "Badi'atul Noor!" Taji muryan Sultanate, bata yi mamakin jin muryan ta ba, yo ai tasan za a rina wai an saci zanin mahaukaciya. "Ina kike? Anya kina da imani kuwa? Ki raba mutum da Matansa da Yaransa anya akwai Allah a cikin lamarin ki?" "Hmm ga wuri nan zauna" ta fada mata, domin bata cikin rigima irin na tsofi, D'anta ma gashi nan haushin take ji. "Akan me zaki saka shi anan ya zauna bai da wasu matan ne? Ko so kike Allah ya saka min D'a a wutan lahira?" " Ko daya Sultanate, ai ga danki nan sai ki saka shi a gaba ya bar sashina" ta fada tana kafe Sultan da idanu. Wani kalar tausayi ya koma har ga Allah baya son ya koma, domin masu bibiyar sa suna cikin jikin sa. "Mama ki bar ni anan." Ya fada yana kallon Badi'atul Noor, dauke kai tayi tana faɗin. "Sultanate kar ki yarda ki dauke shi ku bar min nan" "A'a ba zan tafi ba" "Na rantse da Allah sai ka bar nan!" "Ba by inea zani, Mama ki gaya matan babu inda zani" idan Badi'atul Noor ta fadi magana Sultanate sai ta kalle ta, idan Sultan yayi magana sai ta kalle shi, kafin kace me sun mai da ita karamar mahaukaciya. A hankali ta mike bata ce musu kar ku daina ba, cewa tayi. "Allah ya baku sa'a idan kun kara ganin kafana ku min duk abin da kuka gadama ai ku ba yara ba ne sai ku cinye kanku " ta saka kai ta fita, kallon juna suka yi, "ka tashi ka bi bayanta " "Don Allah kar ki rufe min gidan na hada ki da Allah" tab'e baki tayi tana faɗin. "hmm da Sultanate Waziri ya gana ranar da bom ya tashi a kofar masarautar nan, kafin nan ya gana da kai me ya faru a tattaunawar ki?" Kura mata idanu yayi kalaman SAN yana dawowa kansa daya bayan daya. _Har ga Allah akwai zalinci matukar baka bincika al'amarin Yaranka ba, wannan gubar ba a cika samun shi a ko ina ba, asalima sinadarin da aka yi amfani da su, yawun maciji da gubar kwad'o, duk wanda ya shirya wannan gubar ba karamin shaidani ba ne." "Dawood ya zan yi? Wallahi tsoron tashin hankali nake idan aka fara bincike dole hankalin mutane zai tashi bana son abin da bai kai ya kawo ba ." "Kenan sai ka sadaukar da rayuwar Yaranka domin kar mutane su." "Wannan wani irin zance ne? Taya zan sadaukar da rayuwar Yarana? Ka duba dakyar nayi maka kama da wanda ya sayi duniyar sa sama da lahiran sa ne? Tow tabbas zamu ne mi mafita matukar kana son a hukunta masu laifi, bani lokaci na gama hada hujjojin da ya da ce_ Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya kura mata idanun ya ce. " Tabbas mun yi magana da ta shafe mu, amma kuma ban kawo kome ba, domin ma bar shi akan zai bincika abin da yake faruwa." Daga haka yayi shiru Badi'atul Noor, tana da kwalin Master degree a fannin law, duk da tayi karatun amma miji irin nata, ya hanata aiki. Muryan Sultanate suka kuma ji tana bala'i. "Badi'atul Noor! Zo nan akan me Aliyu zai ji amsar soyayyar Saratu?" Fitowa tayi tare da saukowa kasa. "Saboda naga bata dace da ita ba, maganar da nake dake yanzu ana kan maganar sa da Latifah yar wurin Dan uwana." Daga haka ta zauna tana kallon Sultanate. "Ni na haifi abuna, ke kuma kika haifi Ubansa ina ga a nan a bar ni nayi iko da abuna" "Badi'atul Noor ni da tsufa na kike min rashin mutunci" "ko daya tsufar taki ce tasa nake binki da lalluma." "Ai shi kenan amma ki sani ko mutuwa yake ya dawo sai ya aure ta." "Bayan ya auri wacce na zab'a mishi." Fuuuuu Sultanate ta bar falon. Wani abu ne ya tsaya a ran Badi'atul Noor a hankali ta koma sama, "ke dai baki gajiya da rigimar Mama kina d'aga mata kafa. Mahaifiyata ce." Kallon shi tayi na wasu dakikai kafin ta ce mishi. "In sha Allah" kirar ce ta shiga. "Boy yanzu nake wani tunani, kana da wacce kake so ne? Ina son kafin azumi an yi bikinka da itama." Murmushi yayi ya ce mata. "Zan turo miki sako ta e-mail dinki, amma bata magana bata ji da kunne daya" "Allah Sarki, doughtier ta tafi dota ta dawo." Murmushi tayi a hankali ta ce mishi ya sunan ta. "Lucky" "kaniyar ka, ba musulma ba ce?" "Sa'adatu Aminu Fulani" "Fulani zan kira ta." (Idan kin so ki kira ta da Shanuwa 🤣🙄 akwai Charm prince Abdul Hakim Sharif Hamidu yana can yana suma akanta 😏🤔😏 Son head kawai, ji wani tsohon munafinci wai Lucky yo na zata jikar mangof ce ma😙) "Ya kamata a tura manya daga nan" "eh amma nafi son ta kare makarantar ta, asalima ina son tana gama secondary sai ayi ta zo nan akwai wani jami'a a Canada can zan kaita." "Kace yanzu take karatu ma?" Murmushi yayi sannan ya ce mata. "Eh Ummi Yasu Annur da Nur da Junior? Ya cikin Hamdiyah?" "Duk suna lafiya suna tare da Zuwairah ita ke kula da su" "A'a Ummi me yasa baki bar su a kuda dake ba? Ummi su dawo ɓangaren ki da zama wallahi gidan nan dai-dai yake da jahannama, don Allah a dawo su, idan da hali ko abincin su kece zaki kula da shi don Allah Ummi na" ji tayi kamar ya daureta da jijjiyar ta, "Zuwairah mun ji ma da ita, kar ka saka min rashin jituwa da zargin ta" "Ummi ba mutane ne abin ki ba, zukatansu ita ce abin tsoro, Ummi ban yarda da kowa ba sai kaina sai mutanen sokoto don Allah ki dawo su wurinki " "shi kenan za ayi haka." *** Ranar da suka dawo hutu, bata koma makaranta ba, tana zaune a tsakar gidan su. Nazif yayi sallama dauke da manyan jakunnan. Kallon shi tayi na wani lokaci kafin ya sake murmushi. Ta mike tana me nuna mishi ya tsaya ta dauko taburma ta shimfida mishi. Zama yayi ta koma zaure ta dibo mishi ruwa a randar kasa, sannan ta kai mishi duk ta rasa me zata bashi. Zama tayi akan kujera yar tsuguno. "Sannan ya aiki? Nana ta ce kai ma kana birnin ne?" Gyad'a yayi mata yana kallon yadda ta kara girma ya waye ba kamar da can ba, duk da a can baya ma, tana daga cikin yaran da zuwa Sokoto bai basu wahala, domin akwai yayenta can. Mika mata wata takarda yayi, ta amsa tana mishi kallon tambayoyi, sannan ya tura mata jakunnan. Farkon kaita makaranta da irin wadannan kayan ya kaita, visiting na farko da shi ya kawo mata, lokacin da aka dake ta da kayan ya dawo da ita makarantar. Jan ledar tayi ta rungume tsam, hawaye yana zuba mata. Ji take kamar shi take rungume da shi. Kara rungumar kayan tayi. Kamar ya fahimci tambayar ya nuna mata takardan da ya bata, "Malam Nazifi kai ne a gidan mu?" "Eh wallahi Inna Laminde ni ne, na kawo sako ne wurin Sa'ade" ya mike. "ikon Allah ba dai tafiya zaka yi ba?" Eh yau zan koma na je makarantar su aka ce bata dawo ba shi ne nazo gida na kawo mata sakon" mikewa tayi itama tayi ta mishi godiya. "Allah sarki baka jin labarin bawan Allah nan Gadanga?" "Yana kasar waje shi ya bani sako na kawo mata" "Ayya ka gaida min shi don Allah" "zai ji Inna Laminde sai an jiman ku" "Ayya mun gode ka gaida gida." Da sauri Sa'ade ta shige dakin su, ta bar kayan ya awurin jikinta har rawa yake. *Amincin Allah ya tabbata a gare ki! Sa'addah da fatan sakona ya iso gare ki! Nasan yanzu kin girma, ina sane dake abubuwa dayawa sun faru a cikin su har da kewar ki. Ina kawayenki ki gaida min su. Ki gaya min Innata da Baffa, ina rokon ki don Allah ki jira na kusan zuwa gare ki ki adana min kanki Aliyu Abuturab sulu gambari kiyi hakuri kinji, kuma don Allah kiyi karatu kiyi karatu sosai* k'amk'ame takardan tayi tana kuka, kuka sosai take, haka Inna ta shiga dakin ta rungume ta, haka ta cigaba da kuka. Bubuga bayan ta Inna take, sai da tayi shiru. Ta tambaye ta, "ke da shi kuna son juna ne?" Zaro idanu tayi tana kallon Inna, idan ta ce tana son shi ba mamaki Inna ta watsa mata mari, nuna kanta tayi sannan ta ce mata " Ni kewar shi nake" gyara zama Inna tayi ta ce mata. "shi wanda yake zuwan nan meye a tsakanin ku?" "Bana son shi" ya fada har tana shirin fara kuka. "Ya isa babu me miki dole" Haka tayi ta rarrashinta, har taji muryan Malam Aminu a tsakar gidan. "Waye ya kawo." Makalewa maganar tayi sakamakon jin kamshin turaren kayan kamar yasan me ita, wani kwalalo idanu waje yayi tare da tuma tsalle. "Ina yake?" [12/06, 8:06 am] usmanlauratu71: 35... jikinsa wani irin rawa da makyarkyata ya dauka, kamar ya sake fitsari a wandonsa. "Malam lafiya?" Cire idanu yayi yana kallon. "Kayan waye?" Wani irin kallo Inna Laminde ta mishi. "Kayan waye na tambaye ki?" Ya fada da ƙarfi, "Kayan Sa'ade ce da Gadanga ya turo." "Billahi ba a gidana ba, na gaya miki gaskiya ba a gidana ba, dauke tsiyarsa ki fitar min da shi" "ban gane ba malam, kayan Aliyun xan fitar ko me?" "Eh kayansa zaki fitar min da shi, yaron da bai ga girma da mutuncina ba, shi ne zaa kawo min kayanshi gidana? Yaron da ko sunan shi naji kawai sai naji kamar zan mutu? Ke raba kanki da shiga harkan wannan Yaron bani kayan daga yau alakar da take tsakanin ku na yanke" sororo tayi tana kallon rashin arzikin da Malam yake lafta mata, ya dauki kayan kuwa zai fita da shi tayi maza ya sha gaban shi. "Bani" ta wabce kayan a hannunsa, "idan kana da zuciya ka biya shi dubu ɗari ukun sa sai kazo muyi tsayayyan magana da kai " ta wuce daki da kayan, fuuuu yayi hanyar waje, gidan Mai gari ya nufa yadda zaka san Mal Aminu ya shirya da rigima yana nufar gidan mai gari, kai tsaye zauren da dattijon yake zama ya faɗa, yana daga tsaye ya bude baki da karfi ya ce." Na rantse ka gayawa wancan Yaron kar na kuma ganin sakon shi wurin Sa'ade, domin na mata miji, kar na kara ganin sakon sa." Tashi zaune mai gari yayi daga kishingid'e da yake ya kura mishi idanun kafin ya janyo tabarau dinsa ya ce mishi. "Ban fahimci inda sakon ka ya nufa ba, Malam Aminu? Zauna sai muyi magana daya" zama malam Aminu yayi ya ce. " 'yata Sa'adatu na mata miji, a koda yaushe aurar da ita zan yi bana son na kara ganin aikan Aliyu gidana" ya fada da wani irin kwarin gwiwa. Jinjina kai mai gari yayi daga bisani ya ce. "Tow ina kudinsa da ka karba akan ka sayar mishi da Sa'ade?" Murmushi Malam Aminu yayi ya saka hannu a cikin aljuhun rigarsa ya shiga ciro kudi daya bayan daya ya ajiye a gaban mai gari. Domin a cikin laida suke, yayi alƙawarin tsaf sai ya rama iskancin da Abuturab ya mishi bayan yaga Sa'ade, koda Abdul Hakim ya zo, kuma yana bari da kudi yasa shi hada na hannunsa da wata saniyarsa da ta kasa, ya sayar baki daya ya had'e dubu dari biyu har da na abubuwan da ya mata da zata makarantan ya biya, "gashi nan bana son wani alaka ya kuma shiga tsakaninsa da 'Yata. Na raba tsakanin su na kuma raba duk wani abin da yake gani 'Yata kuwa na mata miji daidai da ita." "Malam Aminu kar ka kashe mata karatu, shi yasa aka barta tayi karatunta" "kar na barta tayi karatu kace bayan kai a nan duk Yaranka mata babu budurwa a cikin gidan ka ko ba haka ba? Nace akwai budurwa a cikin gidan ka? Ni wani dan iskan ne ya haifa min ita? Aure zan mata na gama magana ta" daga haka ya mike, domin ya gama magana baya jin zai kuma magana.. ***Abdul Hakim, tunda Hajiya Daulah tace ba zai yiwu soyayyar shi da Sa'ade ba, ya yanki jiki ya fadi. Aka nufi asibiti da shi. Hankalin kowa ya tashi, domin bata zata zai iya faduwa akan soyayyar yarinyar ba, sai da Dr Sharif ya zo, likita yake gaya mishi halin da yake ciki domin yaje har office din Likitan ne. Zama yayi ya mika masa hannu suka gaisa. "Dr da fatan ciwon sa ba kar ta baya ba ce ko?" Zare glass din idanunsa yayi ya ce masa. "Alhaji Sharif maganar gaskiya meye kuke bukata haka a rayuwar sa? Me yasa kuke matukar son kanku ne? Sau da dama inda ake da irin wannan case din sai kaga suna bin majinyacin a hankali amma mutuwa sai ta dauke musu shi, ku kuma kun samu yayi tsawon rayuwa shi ne zaku kashe shi? Hmm ruwan kune ku bashi abin da yake so, ko ku bar shi ya mutu" jikin shi ne yayi matukar sanyi. "In sha Allah za ayi duk yadda kace." Shawarwari likitan ya bashi sannan ya fito dakin Abdul Hakim din ya koma ya zuba masa idanu yayi na wani lokaci kafin ya gyara tsayuwarsa. Shafa kansa yayi yana jin damuwa sosai. Fitowa yayi ya zauna a kusa da Hajiya, ko Allah ne yaso ta fadi sanadin faruwar al'amarin kawai kamar an matse bakinta, ta shiga bashi labarin abin da ya faru. Kura mata idanu yayi kafin ya ce mata. "Idan har haka shi ne gata tow wallahi you failed it, duk abin da yake faduwa na miki adalci a matsayin ki na uwarsa baki gani ba, Indai auren Sa'adatu shi ne mafarkin Abdul ni na mishi alkawarin cika mishi burin sa." "Wallahi ba zai auri Yar talakawa ba" "dariya yayi tare da kallon ta, ai abin daɗin ba iya talaka ba, kurma ce ya gani yana so sai ki yi duk abin da zaki iya domin dakatar da haka, wallahi kika zafafa akan wannan auren naki auren sai ya girgiza." "A wannan condition dina shi kace min kurma zai aura? Hm maji magani an binne tsohuwa da ranta " daga haka ya mike tana barin asibitin, wasa wasa karamar magana ta zama babba, domin kuwa Hajiya Daulah taki yarda da maganar auren shi, inda ta kafa hujjar cewa idan wani abu ya faru na gaggawa taya zata iya fahimtar shi? Ko faduwa yayi taya zata gane? Al'amarin da ya kai har kamar zasu rabu, dakyar yan uwansa suka shawo kan rikicin, shima a lokacin yake gaya musu ita Sa'aden zabin sa ce don haka duk abin da zata yi tayi.kawai aure babu fashi. Kwana biyu Abdul ya farka, a lokacin ta bijiro mishi da cewa. "Matukar kace yarinyar ce zaka aura tow ka dawo min da kome nawa, har takardan makarantar ka" zai bude baki yayi magana Abban shi ya shigo dakin. "Ka hada mata har da yarinyar da ta aura maka, ka sake ta." A fusace ta kalli Dr Sharif. "Wai me kake nufi ne da ni? Gaya min me kake nufi ne da ni?" "Abin da kike nufi. Taso muje sun sallame ka " ya hada kayan Abdul din,. A wannan karon ita kanta ta razana da matakin da mijinta ya ɗauka domin har ga Allah tana son mijinta. Amma girman kai ya hanata gane haka gani take idan ta kwantar da kai zai mata wulakanci. Akan Idanunta ya tafi da dan sa takaici kamar tayi ta ihu, har gidanshi ta bishi amma kishi da alfahari ya hanata shiga cikin gidan. Haka ta juya abin ta. Kwanankin da suka biyo baya, sauki sai Abdul ya samu, don haka ya zauna a gida yana kara murmurewa, Dr Sharif da wasu manyan mutane, musamman yan garin Binji suka yi tattaki har garin Binji, suka samu hakimin Binji. Suka tafi har garin Maikulki. Inda suka sauka a gidan Mai gari. Bayan an gaisa kafin aka dauko zancen abin da ya kawo su. Shiru Mai gari yayi, kafin ya ce musu. "Tow Allah yasa haka shi ne mafi alheri, a kira Mahaifin ta." Mai gari ya tura wani jikansa me suna Garba, can kuwa sai gasu tare da Malam Aminu. "Ikon Allah wannan ba shi bane ya ce yar shi zata bara ba?" murmushi mai gari yayi, sannan aka dauko abin da ya wuce anan Dr Sharif ya amsa yana faɗin. "Tabbas ni na saka hannu akan a kawo malamai garin nan, na turawa me girma Gwamna." Kura musu idanu Mai gari yayi baki daya wanda ya fi dacewa da a ambaci sunan shi Abuturab ne, amma sanadin abin da ya faru, an jingina kome akan Dr Sharif. "Tow abin da ya kawo ba wani babban al'amari ba ne, ina da yaro ya ga Sa'adatu yana so, shi ne na zo niman mishi izinin niman ta " dake malam Aminu bai da kunya ko ta sisi balle anini yayi carab ya ce. "An bashi Ubangiji ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyiba." "Tow Alhamdulillahi da ayi ta jeka ka dawo mai zai hana a daura auren sai daga baya ayi bikin ba, amma ayi ta jeka ka dawo ai abu dad'i." Dr bai tab'a zatan al'amarin zai zo mishi da sauki ba, don haka sadakinta dubu dari cass aka biya, sannan aka aka biya kudin na gani ina so, da kome da kome, goron tambayar da suka zo da ita, ita ce ta koma goron daurin aure ana sallah azhar aka daura auren Sa'adatu Aminu Fulani da Abdul Hakim Sharif Hamidu. *** UK Karfe biyu da rabi, wanda yayi daidai da daura auren, dauki mug zai sha caffeine zai sha kawai kofin ta fadi daga hannunsa, wani irin duka karfinsa take, a hankali ya durkusa yana rike da Kirjinsa musamman gefen zuciyarsa, idanunsa sun yi jajjur, kansa wani irin daukar zafi yayi, kafin kace me zufa mai karfi ya fara karyo mishi, shigowar Tina sabuwar abokiyar aikinsu, ta gansa a wannan halin, kiran sauran abokan aikin tayi, suka d'ago shi ya zauna, idanun shi yayi jajjur kamar wanda yayi kuka. A hankali ya d'ago kai yana kallon agogon hannun sa. "Ko mu kira motar asibiti ne?" "No need I'm fine" shigowar Manager din su ne ya ce mishi. "Mr Ali kana lafiya?" "Da sauki fa, babu wani abu, zan tafi gida ne kawai" ya koma dakin da suke sauya kaya, ya zauna a hankali. Sannan ya ciro kayan sa, zai saka tina ta shigo. "Ali gashi ko zaka sha?" Kura mata idanu yayi sannan ya ce mata. "Thanks " ya saka rigar shi, dama shirt ce. Yana haka sakawa ya juya ya fita abin sa, dake lokacin tashi bai yi ba, haka yaji zai rage tafiya da kafarsa. A hankali yake takawa. Yana jin kamar ya kuma rasa wani abu da yake so, wani irin kadaici yake ji mai girman gaske. Ji yake kamar ya rasa kome. Har yayi tafiya me tazarar gaske, kafin ya tsayar da bus ya shiga, koda ya shiga zama yayi har suka isa Bus stop. Ya sauka ya nufi hanyar unguwar su, a lokacin da ya isa gidan, ya hango ta tana tsaye a bakin window tana kallon shigowar sa, dauke kai yayi ya nufi cikin gidansa yana shiga ya rufe kofar a hankali. Kofar ta nufa a hankali ta tura, ganin ya daura abinci yasa ta nufar dakinsa. Tana shiga cikin ta same yana cire agogon hannun shi. "Me yasa? Me yasa kake son nuna min bani da daraja? Kai ka ce" "eh ni na ce amma kuma na gaya reasons dina, bana son saboda soyayyar Sa'adatu na cutar dake, ni ita nake so,watan watarana zan cutar dake saboda kawai na zaɓi haka a matsayin abin da nake so, koda yau anyi auren ki sani, wallahi babu wani abin da zan yi da ke, na rantse da Allah. Ana aure be domin sauke babban al'amari tare da zama daya, bana cikin maza masu sha'awar mata barkatai, kin gane a tsarin rayuwata ban cika son cin kowani abinci ba, abinci daya nake son ci daga kansa bana jin wani kwadayi ko na wani wurin " shi yasa nayi adana abincina zuwa lokacin da zanci ya huce" "Abuturab kana nufin bana cikin tsarin abinciin da zaka ci kenan? " "Gaskiya kan, baki cikin tsarin abinciina" daga haka ya mike zai wuce. "amma saura sati biyu auren mu zaka iya gaya musu?" Juyawa yayi ya kalleta. "Ni mutum ne mai gudun zuciyar iyaye ba zan iya fitowa nace musu bana son ki ba, don Allah ina baki shawara ki daina zuwa wurina ki jira a kawo ki " "ka fito kawai kace zaka karbi aurena ne domin iyaye sun maka dole ba?" Murmushi yayi ya wuce abin sa, amadadin tayi kuka ko bakin ciki sai ta fara murmushi mutumin da ya karɓe ka domin iyayen shi tow ba makawa ko aurenka yayi zai yi wuya ya wulakantaka. Murmushi tayi ta juya da baya, ita bata ga laifin sa ba, sai ma kara son sa da take. Dafa bango yayi ruwa na sauka akansa..... Drama never end na woh go give up? 08130269641... [13/06, 4:04 pm] usmanlauratu71: 36... Gidan Malam Aminu. Rabi ce kawai a gida itama ta fitar da mijin ba a gama zancen ta, mijin ne yake gini, suna zaune a tsakar gida, dai ga kawar Inna Larai, Iyar Sani. "Ayiriri! Sa'adatu ta zama Amaryan Abdul Hakim" mikewa Rabi tayi tana faɗin. "Amarya kuma? " Tare da dafe kirjin ta. "Wacece Amaryan?" Ta kuma wurgawa Iyar sani da take kunshe da gulma. "Ke ja can, Sa'ade Laminde ce aka daura auren ta." Inna laminde da take sauraren su a zaure wuf tayi ta fito tana faɗin. "Me kika ce?" "Eh wallahi Laminde yanzu Laminu ya kawo min goro da alawa, kai tabarkallah waye ya tsammanin yar nan zata zama wani abu? Gashi nan an daura auren ta da wai Abdul Hakimu" wani irin kerma jikin Inna ya dauka, tana me zubawa Sa'ade idanu, wacce bata san me ake ciki ba. "babu kome mun gode" ta juya tare komawa zauren, har ga Allah tsiyar Malam Aminu ya fara daure mata lissafi, kwafa tayi ta cigaba da aikinta, tana jin muryan maroka suka ta zuga shi da kirari, ya shigo cikin gidan yana washe baki. "Larai kin ga abin Arziki ko? Ashe ina da yar da zata auri dan masu kudi har haka, Laminde dubi yar albarka." Shewa tana buga cinya, ta ce mishi. "iko sai lillahi, yau ce Sa'a ta zama yar albarka? Yau ce Sa'a ta zama yar da ba zata ba, ai Malam kayi kuskure Billahi Azim yadda ka daura auren nan in sha Allah haka zaka warware da hannun ka, lokacin da danasani ya lullube ka, don zalinci da cin amana har kana da zumman aurar da ita, wato ta zama mutum kowa zai yi tunanin dauka ai yayi ado da ita, in sha Allah idan nice na haifi Sa'adatu da cikina muna nan. Zata dawo min in sha Allah, rayuwar ta bata yi lalacewar da za a aurar da ita kamar yar Akuya ba." "Ikon Allah bakin cikin naci arzikn yar tawa kike min kenan? Tow wallahi in sha Allah mutu karaba tsakaninta da Abdulhakimu" fada sosai kamar zasu daku, bakin Inna har kumfa yake, Sa'ade bata taɓa ganin wannan al'amarin ba, sai yau don haka tayi ta kuka. Da ta tambayi Rabi taki gaya mata, zuwan Harira da take aure a wajen gari ne, domin har an gaya mata an daura auren Sa'ade. Shine ta zo tabbatarwa ai kuwa ta samu gidan ana bala'i. Bakin ciki da ya ishi Inna Laminde gidan mai gari ta nufa, a kofar gidan ya same ta. Toshe bakin ta tayi domin kuka ya ci karfin ta. "Baba mai gari ya zaka ci amanar bawan Allah da yaƙe dawainiya da ita? Kaf duniya babu wanda yayi imani zai rike ta hannu bibbiyu sai shi me yasa ? Yaushe ka zama me irin halin Aminu? Me yasa tun tuni da nace a daura auren ka ki? Shi kenan don kawai wancan yana da galihu da kudi sai a dauki yar a bashi? Wato shi da yayi dawaniya da ita kuma ya zama wawa kenan." Zare madubin shi yayi ya sauke ajiyar zuciya. "Koma gida ki mata addu'ar Allah ya zaba mata mafi alkhairi." Wani irin kuka ta sake fashewa da shi, baki daya jikinta yayi sanyi. "Aliyun ne yace baya sonta?" "Ko daya Asalima ga ginin shi a cikin gidan ana mishi kuma duk saboda ita yake haka, jira yake ta gama makaranta, domin wannan zuwan da Nazifi yayi ya gaya min cewa iya aji biyar zata tsaya, idan an daura auren zai tafi da ita wurin shi tayi karatu, tow waye zai iya da halin mijin ki? Shi daya ne zai iya ban san me zan iya mishi ba." Kamar wata zararriya haka ta kamo hanyar bata san me ake ciki ba, har ta iso gida. Ganin anyi cirko cirko akan Sa'ade yasa ta cewa. "Sai ka kashe ta ka huta kawai Malam ai ka gama sauran. In sha Allah sai." "Haba Inna duk abin da Baffan mu yayi me kyau ne fa, balle kuma mutumin nan ba karamin hidima yayiwa Baffan mu ba, kuma har." "Ke Harirah!" "Inna laminde ta buga mata tsawa, cikin takaici Inna Larai ta ce. "Ke kam kin yi asarar hali na gari, Indai zancen Baffan ku zaki dauka, mutumin da bai da alkibla? Bari na gaya miki wallahi azim kika kuma saka bakin ki akan maganar nan sai na sab'a miki, fita ko bani wuri " kama Sa'ade suka yi zuwa daki, suka shiga bata kulawa. lokacin da ta farka, kallon Innar ta tayi na few seconds, kafin ya fashe da kuka, tana kara rungumar ta. Shafa bayanta take itama tana kuka. D'aga labulen yayi yana faɗin. "Ga sadakin nan na dauki kudin gaisuwar uwa da uba, tow na dauki na Uba wannan kuma naki ne, yawwa zaki bani aron naki zan kai sadaki ne" cak kuka ya tsayawa Inna ta juyawa tana kallon shi. Wani irin murmushi ya kwace mata, ta ce mishi. "Tausayi kake ba ni" daga haka ta cigaba da rarraabin Sa'ade. Haka ya gama surutun shi ya fita, ai kuwa a ranar zazzaɓi ne ya sauka a jikin Sa'ade, domin baki daya ta firgita har ga Allah bata kawo aure a kanta ba, kawai abu yazo lokaci guda, karatunta fa? Wannan abin ya tsaya mata a kai, babu abin da yake kara sakata kuka da tashin hankali kamar yadda bata san waye mijin ba, burinta nason tsayawa da kafarta ya lalace. Haka tayi ta kuka, tow ina Hammayo ya tsaya? Me yasa Hammayo bai zo ba? Hammayo! Ta kuma fashewa da wani irin kuka, Hammayo shi ne sunan da tasakawa Abuturab. Kwana suka yi basu gane kanta ba. Sokoto. A gajiye suka isa gidan Alhaji Hamza Marafa ya kalli Dr Sharif. "Kasan me? Dattijon nan bai so auren nan ba, naki maka magana ne, amma kamar akwai abin da yake ganin shi ne daidai ko an yi kuskure " zare medical glass din shi yayi ya ce mishi. "Ni ma na fahimci haka, sai dai ban kawo kome a raina ba, na zata ko irin yanayin mutanen mu ne" "ko daya ba haka ba ne, kasan na rigaku fitowa, ina jin wani yana faɗin. "Amma dai Malam Aminu bai kyauta ba, auren Sa'adatu da Abdul Hakim kamar akwai son zuciya a cikin sa, domin akwai sadakin wani aka daura kuma ita ake jiran ta gama karatu Allah ya kyauta. Daga haka na fahimci akwai matsala. " Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce mishi. "Ban sani ba, kuma kasan matsalar Abdul Hakim, yadda ciwon ta kama shi, ga shi ba samun kyakyawar kulawa yake daga mahaifiyar shi ba, yana son yarinyar sosai shi yasa na tsaya akan zancen." "Amma dai maganar gaskiya akwai son zuciya a cikin al'amarin idan yarinyar bata son shi ya kenan?" Saka hannu yayi ya rufe fuskar shi. "An tauye mata hakki." " Kaga kenan an yi zalinci tunda har ga Allah dukkan mu babu wanda zai iya yiwa nashi auren dole, ita kuma dake Allah ya haɗa ta da mugun Uba, yasa ya amshi auren babu ko bincike. Kawai kar na zurfaffa ne amma sam uban ba na gari ba ne, idan ka lura ya hana kowa magana shi daya yayi kidar shi da rawan shi. Don Allah idan ka fahimci yarinyar bata son shi, da a zauna ayi ta cutar juna a rabu shi ne masalaha " "in sha Allah haka zaa yi." Har sai yafi ya ce mishi. "Don Allah ka saka idanu akan Daulah da yaranta domin ba daraja ce da su ba, na san halin Daulah." "In sha Allah haka za ayi " shiga gida yayi shi kuma ya wuce. Baki daya jikin sa ya mutu da al'amarin daurin Auren, koda ya isa gidan Aunty Fareedah a can ya same Abdul ya bashi labarin auren. Sannan ya tsare shi ya gaya mishi gaskiya tana son shi ko bata son shi, fur yaki fadar gaskiya. Haka suka yi ta lissafin abin da za ayi tunda tana makaranta ne, sai ta gama za ayi bikin. "Gaskiya ni a bani ita kawai ba sai an yi bikin ba, daga gidana zata na zuwa makarantar " "A'a Abdul ba zan yarda tauye mata hakki ba, idan kasan ba zaka bar ta tayi karatu ba a barta sai ta gama, tunda kaga uwarka ba son ta take ba" "in sha Allah zata yi, ba zan hana ta ba" "shi kenan, Fareedah zan tura miki kayan akwati da duk abin bukata." "Tow shi kenan." "Aunty zan kara miki wani abu." "Allah ya isa tsakanina da kai wato don cutarwa shi ne zaka aura mishi kurma? Me yasa baka aure ta ba, me yasa sai Yarona idan yana ɗakinta ciwon shi ya tashi waye zai gaya mata? Wallahi matukar ina raye ba zai tab'a zama da ita ba na gaya muku, kai kuma idan har ka zabi mata min rai ne kayi haka, na baka nan awa ashirin da hudu ka turo min kome nawa da na maka, ko kuma sakon ban hakuri da takardan sakin ta." Inji Madam Daulah. "Kayan ki zai mai da miki su, amma saki kan babu wannan zancen Allah ya kara miki lafiya kiga yan dagwai-dagwai din Ubana da Sa'adatu sa'ar mata." Sunkuyar da kai Abdul yayi yana murmusawa a ran shi yana faɗin *Sa'a tafi manya kaya* Aikuwa Madam Daulah ta hau ruwan bala'i kamar zata cije kanta (wai nace me yasa ba zaki ciji yan GRP ba😬🌚) masifa yadda take shiga ba nan take fita ba, don jaraba har tsalle take. Kamar zata kama wuyar wani da dukka. *** Kwara. Da sallama mutumin ya shigo falon kasa, ya gaida Ummi, sannan ya mika mata file din. "Sultanah ga aikin da kika bani " "na gode sosai, amma ya labarin." Kallon agogon hannun sa yayi ya ce mata. "Kin san dake wani lokacin labarin da yake kasa shi ne kawai yafi armashi, amma wanda yake kasa bai da armashi wani lokacin ma babu dad'i idan aka ji ko aka gani " ajiyar zuciya ya sauke sannan ta ce mishi. "Kenan duk zagayen babu wani labari?" "Akwai amma so samu ne a nutsu domin jin labarin, Sultan kar ki manta shi labari kala-kala ne, kar ki sake ko ki bar wani gagarumin labarin da zai bazu nan da wani lokaci " kallon shi tayi na wani lokaci kafin ta ce. "anya zan iya zan iya sauraron labarin nan? " Mikewa yayi cikin girmamawa ya ce mata, ga kaɗan daga cikin labarun ki nazarce shi a hankali ta haka ne sauran labarun zasu zo da sauki, don Allah kar yawan shi ko tsawon shi ya hanaki nutsuwa, idan kika ji tashin hankali ki ajiye ki huta, na bar ki lafiya." "Na gode kasan dai yanayin garin akwai zafi ka kula da shan ruwan jakara." "Ko a birnin ba a shashi ba." "Tow a karkara ba a agaza shan sa ba." Ta karasa mishi.(Sultanah Badi'atul Noor kar ki sayar damu mana a juyayyen bayani......🙄😏) 08130269641 [14/06, 9:46 am] usmanlauratu71: 37.... Tashi tayi daga falon ta koma ɗakinta, tana nazarin rubutun. A falon kuwa Zuwairah ce ta wuce dakin su,tana bude dakin suka ci karo da juna. "Hmm! Dama kina dakin ne?" "Eh mana, ba gani ba ai ina nan kawai dai ina jiran sultanah ta bar falo ne nayi shara." "Amma ai naga baki jima da yin shara ba, sannan zaki sake wani?" "Tow ai goge goge zan yi na saka turaren wuta." Shiru suka yi kafin Zuwairah ta bata hanya. "Mama Zuwairah akwai abin da kike boye min ne?" A razane Zuwairah ta juya tana hararanta. "Me zan boye miki jeki kawai " fita tayi Zuwairah ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta dauki biro tayi rubutu. Ta bude window ta wurga, a can bayan window akwai yan mata bayi suna aiki, dauka daya daga cikin su tayi ta dauki kwandon sharan ta, ta bar wurin tana isa hanyar da zai kaita ɓangaren Sultanate, ta d'aga wani Flower pot ta ajiye a tayi ya fitar ta, me sharan wurin tana zuwa ta fara share wurin, sannan ta d'ago pot din kamar zata share ta dauki takardan, ta wuce da shi bangaren Hajiya Turai. Daga can aka sake ɗaukar takardan zuwa bangaren Hajiya Mariyah, daga can aka wuce da shi falon Hajiya Badariyyah, aka saka a kan Dinning table dinta, har sai da Irif ya dauka zai yaga Tabawa ta amsa, ta saka a cikin abin shara. Ta kai can inda zata juye sharan, haduwa suka yi da Sarkin fada. Bangaje shi tayi, "kayi hakuri" ta wuce abinta. "mara kunya mara tarbiyya kawai, sai da ta tsinka min takalmi" ya tsuguna ya dauki takardan. Ya soke a aljuhunsa, yayi gaba yana mita. Bangaren Badi'atul Noor ya nufa yana mita. Saka facemask yayi a hancinsa. A can sama kuwa Maganar Auren Abuturab da Latifah. Ya kaita falon Sultan da yake saman. "Barka da warhaka yallabai, ya jikin naka?" "Alhamdulillahi, da fatan ba rashin kirki ya kawo ki ba?" Ya tambaye ta, dariya tayi ta zauna. "Allah ya baka nasara ba abin da ya kawo ni ba kenan." "Ok Ina jinki" ya ajiye Jaridar hannunsa ya zuba mata ido. Murmushi tayi sannan ta ce mishi."Dama maganar auren Baba karami ne, mun yi magana da Yayana akan zancen sai yake gaya min ashe Sultanate ta tura Suhailah da Yarta su daidaita kansu da Baba karamin shi kuma ya ce baya sonta sai Latifah. Shi ne nace ko za a tura galadima ya tuntube Baffa Hadi." "Tuwona mai na zaki yi kenan?" Murmushi tayi tana faɗin. "Baba karami ya girma, kuma ba dadi ganin shi haka, duk da ya gaya min cewa yana da wacce yake so amma yarinya ce bata magana makaranta ba. Latifah ya ambaci sunanta ne kawai don kar a takura mishi ya auri Sarah" "kenan me yasa ba zaki goyi bayan shi ya auri Sarah ba?" Gyara zama tayi sannan ta ce mishi. "Ba haka ba ne, sai dai kuma ba zan mishi dole ya aure ta ba, ita kuma Latifah da kanta ta gaya min idan ba shi ba, ba zata yi aure ba, a wani lokaci domin farin cikin wasu zamu iya sadaukar da namu farincikin, shi yasa nake son ya aure ta, matar da take jin idan ba kai ba, sai dai ta rayu babu aure tafi matar da ita da danginta su zasu bukaci haka, sannan kasan yadda muke takun saka da Suhailah ce zan yarda D'a na ya auri Yarta? Ai kasan ba mai yiwuwa ba ne." Murmushi ya yi sannan ya ce mata. " Ku mata al'amarin ku sai ku, ni bani da matsala akan haka, amma ku matsalar ku babba ce, musamman idan baku san surukar ku, in sha Allah zan tura sai ayi kome cikin sati Uku masu zuwa amma ba zai tako gidana ba." "Baka da case" ta fada a hankali, sannan suka shiga tattauanawa. *** Maikulki. Kwana biyu mai kyau aka dauka ana rigima a gidan malam Aminu, wanda shima ya kafe sai dai ayi uwar watsi, a ranar na uku ne Abdul ya zo. Har dakin Inna Laminde aka mishi iso, sama sama suka gaisa da Inna Laminde, shima don kawai kar ta zubda mutuncinta ne yasa ta kula shi amma kuma tabbas ta bata son shi, sanye yake da wata danyen boyel, blue black, an zuba aikin a gaban Babban rigar. Daga yanayin fuskar Inna ya fahimci bata maraba da shi, duk sai jikin shi ya mutu. "shiga nan dakin, bari na saka a taso maka ita " inji Malam Aminu, shiga dakin Inna tayi wanda yake gyare tsaf, ya zauna sai kamshin turaren tsinke yake duk da bata san da zuwan shi ba, sai dai Sa'ade ta gyara dakin. Zama yayi yana kallon dakin. Da sallama Malam Aminu ya shigo ya ajiye mishi kwanon sha, cike da ruwa. Yana fita sai ga Inna Larai da wani kwanon shan cike da madara dafaffiya, sannan ta fita, dama abincin gidan dambu ce. Bata gama ba. "Ina Sa'an take?" "Tana dakin su Malam" "maza tazota bana son sakarci ga mijin ta yazo, ta zo ta nime albarka" ya band'e labulen dakin yayi tana kwance. Tashinta yayi ya kira ta. Bata san me yake nufi ba, don haka ta mike, tare da saka hijab ta bishi. Inna tana kallon su ba karamin danne zuciyarta tayi ba, amma tabbas ranta ya masifar b'aci. Dakin ya nuna mata, kallon sabon takalmi tayi. Idanunta ne ya cika da kwalla. ta shiga bayan ta buga kofar dakin. D'ago kai yayi yana kallon ta, kanta a sunkuye tana wasa da hijab ɗinta, hawaye na zuba mata. Zama tayi a can nesa da shi, gyara babban rigar shi yayi ya matsa gaban ta, inda ya cusa kanta a tsakanin cinyoyinta. Hannun shi ya kai bayan ta, da sauri ta cire kanta tare da ja da baya, murmushi yayi ya ciro littafi da biro ya rubuta mata. "kiyi hakuri ki amshi soyayyata" ya tura mata. Kallon shi tayi, ta dauke kanta. "Please ki ce min wani abu!" Nan ma shiru tayi bata mishi wani alamu da za fahimci zata mishi reply ba. "Tow shikenan, amma ni zan iya rungumar ki?" Kallon shi tayi lokacin, ta ja da baya, tana girgiza kai. Sake rubutun tayi yayi ya ce mata. "Tow ki min magana" daukar biron tayi ta ce mishi. "Bana sonka, Bana kaunarka, don Allah ka rabu da ni" murmushi yayi sannan ya rubuta mata. "ina sonki sosai, ba zan iya rabuwa da ke ba." Hawaye ne ya zubo mata. "Gara na mutu da na zauna a matsayin matarka" "A'a kar ki yi haka" "zan yi haka matukar baka kyale ni ba" ta rubuta mishi, sannan ta bar dakin. Shiga da abinci Inna tayi da kanta. Ta ce mishi "kaci " "na koshi Inna " murmushi tayi sannan ta ce mishi. " Baka mana adalci ba, kazo da farko tace maka bata sonka me yasa kayi amfani da karfin ka? Zaka iya sayan kome amma shi so ba a sayan sa. Har ga Allah ba zan iya cewa ina ra'ayinka ba, amma ra'ayin Sa'ade ina tare da shi dari bisa dari, kasan me yasa nake jin bakin ciki abin da kayi, saboda lokacin da take da rauni baka sani ba, sai lokacin da kowa zai more ta kasan cewa mutum ce, ba zan ce lallai sai ka rabu da ita ba ba, amma bana jin a raina akwai abin da zai saka ta so ka, domin tana ganin kaso kannka da yawa. Allah ya baku zaman lafiya, amma tabbas ka kashe mata farincikin ta hanyar amfani da karfi wurin aurenta, kuma wannan shi ne zai haifar maka da danasani mara amfani" shiru yayi yana kallon abinciin, a hankali ya mai da idanun shi akan Inna sannan ya ce mata. "Ban san yadda zan yi ba ne, amma nasan naso kaina dayawa, don Allah ki bata hakuri wallahi ina sonta sosai " yadda yayi maganar sai da yasa jikin Inna yayi sanyi. "Allah ya kyauta " "Amin Ya Allah, hmm dama mahaifina ya ce na gaya muku ko za a saka bikin ne nan da sati biyu, saboda makarantar ta." "Ka tambayi Babanta da ya baku auren nawa kuma a wanne" "Allah ya huci zuciyar ki, dama ina son na gaya miki ne ba sai an kawo kome ba, ita nake so ba kome ba" "A'a zamu mata nata kayan gudun gori, Allah ya bada zaman lafiya " "Amin Ya Allah " haka suka yi magana sama sama, ita kan ta Inna ta amshi Abdul Hakim ne domin babu yadda ta iya musamman yadda yake nunawa yana son Sa'ade, amma ba don haka ba babu dalilin da zai saka ta amshe sa. Har yazo tafiya, Sa'ade taki yarda su hadu da ita. Sai bayan tafiyarsa ce Innah ta kira ta. Zama suka yi tana kallon. Riko hannunta Inna tayi ya kalli cikin Idanunta. Ta rufe hannunta ta ce mata. "Ki amshi kaddaran ki " a hankali ta janye hannunta, tana girgiza kai, hannu ta saka a wuyar ta tayi mata alamar ta rantse da Allah, ba zata amshi auren shi a matsayin ƙaddara ba, bata son shi, ba zata zauna da shi ba. Idan kuma aka ce sai ta zauna da shi gara ta mutu kowa ya huta. Kura mata idanu tayi, ganin yadda take kuka yasa jikin Inna yayi sanyi sosai. "Kiyi hakuri" kuka tasawa Inna ta tashi ya haura gadon bonon Inna tana me juya mata baya. *Hammayo ka kyauta da ka tafi ka bar ni* ta fada tana me fashewa da kuka, *Ba zan tab'a son shi ba Inna ba zan so shi ba, na rantse da Allah ba zan so shi ba* abin da take fada kenan a ranta tana kuka. "Kije ki sallame shi nasanwyana waje" ko motsawa ba tayi ba babu yadda bata yi da ita ba, amma fir taki tashi. Haka ya gaji ya tashi ya bar garin. Haka Kwanaki suka ci-gaba da tafiya. Har aka samu sati biyu, inda aka yi yar karamar biki domin ita kan Inna bata yi taro ba, wadanda suka ji labarin ne suka zo, bayan la'asar aka ɗauki amarya zuwa Sokoto. Allah ya bada zaman lafiya mu zo suna. *** Makaranta kuwa. Husnah da Kubrah suka dawo, babu Rahilah da Sa'ade, ba karamin damuwa suka shiga ba, musamman Husnah. Kubrah kan na dan lokaci ne, daga baya ta watsar, ta cigaba da harkan gaban ta. Husna kuwa kasa hakuri tayi, har sai da tayi karyan ciwon ciki aka kaita gida, daga gidan kwananta biyu, ta nufi unguwar Yayanta. Koda ta shiga suka gaisa da Aunty Ummi. Leke leke ta ke tana son ganin ta inda Sa'ade zata fito. A dan koyon da Aunty Ummi tayi take tambayarta Sa'ade take nima. Gyada kai tayi, murmushi tayi ta ce mata. "Tana nan shekaranjiya aka kawo ta, an mata aure sai dai idan zaki je na miki kwatance" gyad'a tayi tana faɗin. "Eh zan je" haka ta rubuta mata sunan unguwar, bata kara minti ɗaya ba, ta bar gidan har estate din aka kaita, bata sha wuyar gane gidan ba, dakyar aka batar ta shiga, domin ba a gaya masa wata zata zo ba. Sai da ya kira Abdul Hakim yake gaya mishi wata yarinya ta zo ganin Amarya amma bata magana. Shine ya ce ya barta ta shigo domin yana gida. Da kansa ya fito ya tare ta. "Rahilah ko Husnah?" Murmushi tayi tace masa alamar harafin sunanta. *Husnah* nuna mata hanya yayi daidai fitowar Sophia. "Ikon Allah tunda aka auro kwaila ake rawan kai.....08130269641 [15/06, 10:10 am] usmanlauratu71: 38.... Cak ya tsaya, tare da duban ta ya ce mata. "Ban san cewa akwai lokutan da zaki b'ata domin hango iyakata ba." Ya fada bayan ya rufawa Husnah baya, tsaki Sophia tayi tare da barin wurin, cigaba da tafiya suke da Husnah tana keta rantsatsun falon da suka kawata saman, har suka cimma matsaya a bakin wata hadaddiyar kofa, bugu biyu zuwa uku. Aka yi ana hutu wata budurwa ta fito tana kallon Husnah kafin hankalin ta ya kai kan sa. "Yallabai taki bude kofar" "babu damuwa na gode" matsa musu a hanya tayi suka shiga, nan ma wani aljannar duniya ce, mai matukar ban sha'awa da burgewa, manyan -manyan kujerun alfarma ne zagaye a falon me dan karen kyau. Koda isar su kofar dakin suka tsaya tare da kallon juna. Shiru Abdul yayi bai tab'a zaton zai ji gazawa akan sa'ade ba sai yanzu da yake jin lallai ya gaza a ko ina, ba don kome ba. Sai tun tafiyar yan uwanta ta rufe kofar baki daya ta hana shi kuzari ta hanyar yi masa shamaki da haramta masa ganinta. Tabbas ana iya gyara kowacce kuskure amma ba a tab'a gyara kwalbar da ta tarwatse a kasa reras ba, tattaro kumajinsa da yar sauran kuzarin da suke tattare da shi ta buga kofar a haukace, wanda zai saka ka fahimci ya kai kololuwar b'acin rai da takaici. Anya ba rashin albarkan da mahaifiyar sa bata saka ba ne ya fara bibiyar sa daga kwana biyu da tarewar matar da yake cike da dinbun kauna da shaukin son kasancewar da ita? Amma kuma lokaci guda ta nuna mishi bai da wani amfani, sake buga kofar dakin yayi a karo na biyu, domin yana jin kamar gazawar shi ta kara haifar da wani irin kunya, domin yadda yake tsaye yana lura da yarinyar tana cikin damuwa. Shiru yayi zai kuma bugawa ta dakatar da shi. Duba jakar gefen kafad'ar ta tayi, ta ciro wani sarka, ta saka a bakin kofar, ta tura shi cikin dakin sannan ta koma gefe tana kallon kofar, zai kuma bugawa ta girgiza mishi kai. A cikin dakin kuwa tana zaune a bakin gadon bata san ana buga kofa ba, sai da ta taso ta fito falon ne ta ga kamar ana turo abu a kofar dakin, da sauri ta isa tsugunawa tayi ta dauka tana kallon sarkan hawaye ne ya zubo mata, dama ta gama cin kukanta kenan ta fito, bude kofar tayi ta zubawa Husnah idanu. Bude mata hannu Husnah tayi, dan gudu ta fada Kirjinta tana kuka. Dakin suka koma tare da rufe kofar, sai da tasha kuka sosai, kafin ta mike ta shiga fitowa da Husnah abubuwan ciye-ciye har ta gama, zata bude kofa ta fita, Husnah ta riko hannunta. Komawa tayi ta zauna. "ina zan kai su?" Ta tambaye ta, murmushi tayi hawaye suka zubo mata ta mata alama da ta zauna. Zama tayi tana kallon Husnah dukkan su kuka suke don sakarci, dakyar suka daina kuka, Husnah ta ci kayan ciye-ciyen sannan ta ke gaya mata Rahilah bata dawo ba, anan take tambayar ta taya aka yi tayi aure. Kukan Sa'ade ne ya tsananta sosai. Dakyar ta gaya mata yadda kome ta faru. "Husnah ina da burin karatu, amma burina ya lalace, da farko mahaifina ya nuna bani da amfani yanzu kuma ya aurar da ni ga mutumin da bana son ko ganin shi." Ta gaya mata. "Kiyi hakuri kin ji, ki karbi haka a matsayin ƙaddara." Girgiza kai tayi tana mata alamar da cewa. "Zan amshi kome da sunan kaddara amma ban da wannan, son zuciya ce kawai son kai ce, na gaya mishi bana son shi amma ya ne mi wata hanya domin ya kuntatta min, hankalin shi ya kwanta ya d'atatta min yaji dadin sa, sai me kuma? N rantse zan zauna a gidansa har ranar da zai gaji ya kore ni, don an ganni nakasa ta min dabaibayi shi yasa aka wulakanta rayuwata." Yadda take maganar da Sign languages zaka rantse da Allah duka zata kai nan kuwa zallar bacin rai ce da takaici, dakyar Husnah ta rarrasheta, sannan ta ke tambayar ta ko zata dawo makaranta? Girgiza kai tayi tana faɗin. "Bai zama dole ya na dawo ba."shiru suka yi kafin suka shiga wani hiran, kafin suka mike suka yi sallah, bayan sun idar Husnah ta bata hakuri sosai, sannan ta mike zata tafi, anan suka kuma.rushwwa da kuka, dakyar suka rabu, ta rako Husnah har kasa, ganin Sophia da Kawayenta yasa ta sha jinin jikinta. Haka ta raka har waje, suka yi sallama ta mika mata ledar da tafito da shi. Dakyar ta amsa tana mata alamar . "Zan miki Addu'a Ubangiji yasa ya dawo dake school" gyada kai tayi tana jin wani irin yanayi na kara yawo a jikinta. Tabbas rayuwar ta yazo karshe, tana kallon su Husnah suka b'ace mata, ta juyo ta dawo cikin gidan. Sophia da kawayenta suna ganinta suka ta fara dariya, abin ya bakanta mata rai, amma sai ta maida su mahaukata, ai babu abu me ciwo kamar ka nime kular da mutum ya nuna maka shi ya san kan abin da kake shiri masa. Haka ta wuce sama, a bakin kofar ɗakinta ya tsaya ta dauke kai. Zata shige ya rigata shiga. Mika mata takardan hannun shi tayi wanda ya ga abin da ta rubuta. _Ki amince da soyayya zan mai dake makaranta _ kallon shi tayi fuskar ta kunshe da takaici. Sannan ta juya ta shige abin ta, sake rubutawa yayi ya mika mata. _Nayi miki alkawarin baki farincikin da ba zaki tab'a mantawa ba, ki amince da soyayya ta_ amsar takardan tayi ta rubuta mishi. *ban san yadda zaka gane ba ne, har abada ba zan tab'a sonka ba, batun makaranta kuwa ai tuni na gama idan ina sa rabon na cigaba zan cigaba amma yanzu kan na yafe Allah ya min sauyin alkhairi* kallon takardan yayi ya wani lokaci kafin ya juya ya rufe kofar, wai zai mata barazanar. Kallon shi tayi hannunta harde a kirjinta. Ya fara kokarin cire botirin rigar shi. Dariya tayi sai da fararren jerarrun haƙoranta suka bayyana. Zama tayi tana kallon shi yadda yake wani mutsuke fuska shi nan zai bata tsoro. Sai yaga sam babu tsoro a tare da ita sai ma wani irin kiyayyar shi da yake hangowa a cikin ƙwayar idanunta biro ta dauka ta ce mishi. *Ka bar wahalar da kanka, domin nasan ba kome zaka iya ba kamar yadda nasan ban isa kaucewa ƙaddarata ba, ka koma wurin matar ka ku lallaba juna* daga haka ta juyar da kanta, bata ma son ganin sa. Haka tsaya cak yana kallonta. Tura mata takardan yayi ya ce mata. " _Ki bani hakkina_ kallon takardan tayi sannan ta rubuta mishi cewa *Babu hakkinka da yake kaina domin a shara'ance sai an nime yarda ta za a daura mana aure baki daya baku cika kome ba sai son zuciyar ku* wasa wasa, Sa'ade ta zamewa Abdul karfen kafa, duk yadda yake tsammanin ta wuce haka, duk yadda ya so tankwarata amma ina ta botsare mishi, sannan shi ba zai iya danne ta ya karbi hakkin shi da karfi ba, domin bai da wannan kwarin da karfin zuciya. Haka zaman su ya kasance har ya gama kwanakin sa ya fita daga ɗakinta. Babu abin da yake hadata da shi da matar shi. Abinci ne tunda ta lura matar shi ba zata bata ba, ta daukawa kanta girka nata, dama iya abin da ranta yake take dafawa, abin dariya duk kure girkinta taliya ce da miyar jajjage, sai firji din da taga baya rabuwa da kifi, shi kenan ta saka kanta da girka Taliya da miyan kifi. Babu ruwanta da wani girki take da shi ko miji babu ruwanta. Shima jarababbe yayi ta binta yana lallabata har ya hakura ya zuba mata idanu. Zuwan Husnah biyu tana kawo mata ziyara, har da karatun da aka yi kwanta daya a gidan ta koma makaranta, bayan tafiyar husna ne yaga yadda tayi ta kuka, tana kara rungumar litattafan. Juyawa yayi ya koma dakin sa, ya kira Hajiya Daulah. Tana dauka ta ce mishi " ka sake ta ne?" "Hajiya don Allah ki bari na maida ta makaranta mun tauye hakkin da yawa idan Abba yaji haka zai sab'a min don Allah Hajiya ki bari na mai da ta makarantar don Allah" "wallahi kwandalata ka tab'a sai na sab'a maka, kai hatta naka ka tab'a ka mai da ita makaranta sai na mugun sab'a maka, ka sake ta zan ni ma maka yar mutunci " "Hajiya ni ita nake so" daga haka ya kashe wayar, haka zaman ya kasance babu dad'i, don ma Sophia bata zaman gidan tana fita aiki ba zata iya kayan takaici ba, shima idan ya tafi aiki gidan sai ya zama babu kowa. Da wannan damar hajiya Madam Daulah ta samu nasarar zuwa cin zarafin Sa'ade, karshe ma don munafinci sawa tayi Abdul ya na kai ta gidan ta, dake kusa da juna ne, wai kar a cutar da ita babu kowa a gidan. Tun safe idan ta shiga cikin gidan bata kuma zama ko shan ruwa sai Abdul ya kusan dawowa aiki za a bata abinci da ruwa, shima don kar ya ganta a galabaice ne. Haka ta shiga kuncin rayuwa ga takuran da Taufiq yake mata, na niman cin zarafin ta. A hankali kwanaki suka haura mako, mako ya rikide zuwa watanin sun shura har ana niman shekara. A cikin wannan yanayin, wata lahadi Inna da su Adda Shamsiyah suka kawo mata ziyara, duk ta lalace, tun da ta gansu ta fara kuka ita kawai su tafi da ita. Ganin yadda ta lalace sun dauka ko ciki ne, sai da suka ga ba alamar kome damuwa ce da ukubar rayuwa. Har zasu tafi Inna ta kalli Abdul da yake ta rawan jiki akan su. Cikin ba'a ta ce mishi. "Abdul ga Sa'ade a karo na biyu zan kuma tuna maka ga amanar Sa'a nan Allah ya taka riko" da mugun karaya ya ce mata. "In sha Allah zan kula" haka ya raka su tana kuka, suka tafi durkusawa tayi a wurin tana wani irin kuka har da jan zuciya. Shima durkusawa yayi a gabanta. D'ago kai tayi tana kallon shi, yana iya cewa a yau ta bashi tausayi sama da kullum. Tayi wani irin duhu, ga uban ramar da tayi, a cikin kasa da wata hudu, tambayoyi ne a bakin shi amma baki daya bai da me bashi amsa, yasan ko ya tambaye ta ba zata bashi amsa ba. Har ta bar wurin yana nazari, kafin ya farga bata nan. Bin ta yayi har cikin gidan. Tana kwance a ɗakinta tayi rubda ciki, domin cikinta ciwo yake mata. Haka ta kwana da ciwon cikin da safe dabya shigo ya ganta a takure ya tab'a wuyar ta, yaji da zafi mika mata hijab yayi suka nufi asibitin, dakyar aka fahimci yanayi da take ciki, domin ulcer da damuwa suka mata yawa, kiran Aunty Fareedah yayi ya gaya mata, kwantar da ita suka yi, sai da Aunty Fareedah tazo ya tafi aiki. Hamshakiya mandiya tana can tana jiran zuwanta don bakin zalinci har da sallamar wasu masu aikinta ta maye gurbin su da Sa'ade, bata ganta ba har washi gari. Babu labarin ta sai da aka yi kwana biyu ta kira Abdul ta balbale shi da masifa ina sa'ade zata bar mata gida da kazanta. "Hajiya bata da lafiya ne." "Tow ta mutu mana, meye ya dame ni? Ka sani ko mutuwa take tana dawowa kawai aikina na sani, lokacin da kuka kwashi kudi kuka basu gaya mata zata yi bautar aure ba ne! Maza ka dauko min ita" "Hajiya gaskiya babu adalci a wannan al'amarin ba zan iya kawo miki ita a halin jinya ba, idan duniya da gaskiya ai su Afiyyah ba haka ake musu ba." "Wani shegen ne zai tab'a min Yarana? Ai kai ma kasan babu shi. Don haka ka kawo min ita ta min aikina" ajiyar zuciya ya sauke, lokacin da yaje asibiti an sallame su Aunty Fareedah ta tafi da ita gida, can ya tafi ya dauke ta suka kamo hanyar gidan, a hanya suka tsaya ya mata hoton passport, haka suka wuce gida, suna shiga ya nime rike hannunta amma taki, yana ganin yadda yake kokarin shiga cikin gidan, murmushi yayi sannan ya taimaka ta. Washi gari ya dauke ta ya kaita gidan Zakaria, shi kuma ya tafi Abuja. Wasa wasa Hajiya Daulah tayi ta zuba idanun zai kawo mata sa'ade amma babu labarin su. Har tsawon kwanaki ashirin, kafin ta dawo ya dauke ta suka koma gidan, kwanan su biyar da komawa, Hajiya tazo tayi ta musu ruwan bala'i, haka ta gama ta bar gidan. Washi gari ya tattara matan shi ya bar mata sokoton zuwa Canada....08130269641 [16/06, 9:27 am] usmanlauratu71: 39... Kwara. Daura auren Abuturab da Latifah aka yi. Wanda iyaye a kowacce bangaren suka tsaya tsayin daka aka gudanar da bikin kamar yadda ake kowacce biki a masarautar musamman shi da ya zama ɗan auta. Bikin da yaso barin baya da kura domin kuwa Sarah Hauka tayi tuburan. Domin saka igiya tayi zata rataye kanta. "Kar ka wani ya zo kusa da ni domin wallahi kashe kaina zan yi na gaya muku, matukar ba a daura aurena da Abuturab ba sai na kashe kaina." "A'a Saratu kiyi hakuri ki sauko za a san abin yi amma kashe kai ai mugun abu ne, sauko ni na haifi Uban Ubansa ni ce nake da alhakin tsaya mishi." "A'a Sultanate ba zasu bari na aure shi ba, har Mamina na saka a gaba muka je wurinsa ya wulakanta mu ua kore mu. Don haka nima zan kawo karshen rayuwata tunda mutane basu damu da mu ba, sai kan su suka sani." "Tow ki mutu mana? Da Yayana suka mutu a jere kin ga na mutu ne? Ko an ce miki barazanarki zai saka na amince a aura mishi ke ce? Tabdijam zauna a sama ki cigaba da zama idan kin so bayan kin mutu ki zama fatalwa karewa kenan" ta juya abin ta, samun wuri ne kawai don ta ja magana da hankalin mutane. Ganin yadda Sultanah Badi'atul Noor ta kwafsa mata yasa kawai ta zarga igiyar a wuyarta. Ihun mutane bai saka Badi'atul Noor juyawa ba, domin tasan ba zasu barta ta mutu ba. Bayan yar karamar tashin-tashina da aka samu haka bai girgiza Badi'atul Noor ba, sai ma kara samun damar nazarin kowa, bayan an watse domin Hamdiyah da Aneesah suka tare da ita da yan jikokinta. Haka aka gama hayaniyar ko a jikin ta, tana bawa Anur abinci Sultanate ta shigo tana huci. "Ya ishe ki haka, duk abin da kike ina kyale ki ne amma yanzu." "Me zai faru idan na cigaba?" "Lallai ma wato don kin ga na kyale ki" "tow don Allah ka da ki kyale ni. Kiyi min duk abin da yayi miki, ina shirye tsaf, aure kuma ni ke da iko da Aliyu ba ke ba, lokacin da na haife shi baki taya ni ba. Don haka ba zaki min iko akan shi ba." Ganin yadda Badi'atul Noor take takarkware tonar masifa yasa ta juya tana faɗin. "Bani da lokacin ki, Allah ya baki sa'ar rashin mutuncin ki ya janyo miki masifa." Bin ta da idanun Badi'atul Noor, tana abu kamar babu ruwanta laifin da ta aikata babba ne, tayiwa masarautar wani irin kazamin laifi da ba za a tab'a yafe mata ba, kuma dukkan akan kare D'anta. Wayarta ce tayi kara ɗauka tayi ta kara a kunnenta. "Wa'alaikumunsalam Auta ka girma fa" "Ummina ban girma ba. Ina kewar ki" "Ni ma haka, ya ji muryan ka yayi sanyi?" "Hmm eh Ummina, tunda na ji labarin an daura auren ne naji jikina yayi sanyi" "Allah ya shirya ka, kana son ayi maka biki ne?" "Kamar dai haka" "inda zaka auri Sa'adatu ni da kaina zan shirya maka bikin hatta fitar Amarya da ango nice please accept this marriage " "I agreed, but Ummina da gaske kike?" "Na tab'a maka wasa ne? Ai duk abin da kake so ni ma shi nake so, feel free bana daga cikin iyaye masu son kai." "Na gode sosai Allah ya raka miki lafiya da nisan kwana" "Amin Baba karami, na Gode." ** Maikulki. Hankalin Inna Laminde baya kwance, hakuri kawai take, amma baki daya ji take kamar ta rasa Saaden ta. Haka yasa yau ta shirya bata gayawa Malam Aminu inda ta nufa ba, amma ta haɗa mata kayan bukata na gida, duk da satin ta biyu kenan da dawowa. Amma zuciyarta ya hanata sakat tana son ganin Yarta wani irin yanayi take ciki ne haka. Shi yasa ta kama hanyar sokoto. Koda ta isa bata yarda ta sauka a gidan Zakaria ba, gidan Sa'ade ta wuce da rabon zata ji hadu da abin da zai d'aga mata hankali. Lokacin da ta isa kofar gidan ta samu Hajiya Daulah tana bala'i. Sauka tayi a dan sahu ta ce musu. "Assalamu alaikum, Sannunki Hajiya" kallonta a wulakance Hajiya Daulah tayi tana faɗin. "Kece uwar nakasashiya yarinyar nan ko?" Kalaman sun daki Inna amma sai ta shanye ta ce mata. "Ba dashi na haife ta ba, samun shi tayi daga sama" "idan kin so ma daga kasa ta haife same shi bai dame ni ba, d'ana da kuka mishi asiri ya auri na kasashiya nake son ku dawo min ko kuma idan na hadu da Yarki na tura ta garin da ba zata dawo ba." Ta fada cikin bala'i. "Sau dayawa harshen mu yana kai mu ya baro, ina me baki shawara ki kiyayye harshen k...." Kauuu ta mari Inna Laminde. Tsit wurin yayi hatta Taufik da yake cikin mota sai da ya zaro idanu. "Matsiyatan banza matsiyatan wofi, shegu masu warin da karnin nono, wallahi matukar na binciko inda Yarinyarki take tare da d'ana sai na kashe ta " shafa fuskar Inna tayi ta yi Murmushi. " Ni kika mara?" "An mare ki zaki rama ne?" "Ko daya ba zan rama ba, sai dai ni na kai karan ki wurin Ubangiji shi zai bi min hakkina. In sha Allah da kafarki zaki zo niman yafiya ta da niman alfarma lokacin zaki fahimci Allah daya yake, ita kuma Sa'adatu. Allah shi zai zame gatan ta a duk inda take bari kiji Allah bai saukar da ciwo ba, sai da ya saukar da magani. Da yarda Allah duk abin da kika shirya Allah zai zama gatar Sa'adatu ba zaki gushe ba sai kin yi kuka da alawadaran halin ki. Gani gaki ga duniya, Allah ya sama yana kallon mu, Mala'iku suna rubuta duk abin yake faruwa." Har Inna ta juya ta ce mata. "Hajiya ki fara karatun kirga kwanankin kukan ki domin zai zo daga inda baki zata ba." "Baki isa ki gaya min magana na kyale ki ba, banza yar kauye wacce talauci yayiwa katuttu." Mai Dan sahu ya leka ya ce mata. "Hajiya duniya dai tafi gabaruwa jima, ki bi a hankali domin wanda ba a haifa ba tana jiran shi balle wanda yayi dakon kanshi da kaya. Allah yana amsar addu'ar wanda aka zalinta ki duba buguyatul Muslim, da alamu duniya tayi miki daurin huhu goro da sannu Allah zai mata sakaya, wannan aya ce a cikin Alqur'ani mai girma." Daga haka ya tadda napep din ya bar wurin. Sai lokacin Inna ta fashe da kuka. " Haba Babah kuka zaki yi? Don Allah kar ki yi kuka, kin gama magana kuka me zaki yi? Don Allah kar ki yi kuka ina zan kai ki?" Ta fada sunan unguwar da zai kaita, rarrashinta yake domin ko ta daure sai kuka ya kwace mata. Haka yayi ta bata hakuri har ya tsaya a hanya ya saya mata ruwan sanyi, tasha tayi mishi godiya. Bayan tafiyar su Taufiq ya fito daga motar ya ce mata. "Gaskiya Hajiya kina da mugun sonkanki, me matar nan tayi miki kika mare ta? Ke baki ji kunya marin da kika mata ba? Itama uwa ce fa? Kika mare ta? Gaskiya Allah sai ya saka mata wallahi." "Ni zaka gayawa magana bani key motana" kallonta yayi. "Kuskuren ki shi zai ja miki danasani Hajiya kuma wallahi sai na gayawa Abba " daga haka ya tafi ya bar ta. Shima me kula da gidan shigewa yayi yana girgiza kai, domin wallahi ta bashi mamaki ashe da ake cewa masu kudi basu da mutunci ashe da gaske ne. Yau gashi nan ya gani da idanun shi. *** UK.... Yar ƙaramar shagali aka yi, makota da abokan arziki duk an taru amma hango yana can shago wurin niman abin da zai rufa mishi asiri. Sai yamma ya taso. Bai dauki mota ba yau, Bus ya bi har zuwa gida yana shigowa ya samu ana ta dan shagali. Sai lokacin ya tuna ashe fa aure aka mishi duk da sun yi waya da Ummi, mutane nata taya shi murna sai murmushi yake musu, har ya wuce part din. Wanka yayi ya shirya tsaf sannan ya saka kayan gargajiya riga da wando ta Sweden cotton gezine, yayi kyau sosai kamar be da damuwa. Haka ya karya hula minista. Sai takalmin shi hafcover made Italia, yayi matukar kyau, turaren zamani ta oud arab. A hankali ya ratsa cikin mutane har ya iso wurin Kawunsa, ba laifi an yi shagali kafin aka watse, aka kawo mishi matarsa. bayan an watse sosai amarya ta zaku domin su sha bidirin kasancewar su ma'aurata. Sai dai kai tsaye Abuturab ya gaya mata maganar da ta hanata sakat. "Kin ga jeki saka kayan ki maza, kizo muyi magana na fahimtar juna kin ji" babu musu ta saka kayanta tazo falon, tana jin motsinsa pancake yake, yana ganawa ya fito ya sakar mata murmushi ya ce mata. "Kin san me? Har ga Allah ni ban shirya rayuwar aure ba, idan kin lura ina hada PhD dina ne, so ni gaskiya bana son damuwa ko wani harkan iyali, ki nunawa duniya dasu Ummi lafiyar mu lau, muna zaune lafiya amma a zahirin gaskiya kowa yayi kokarin achieve abin da ya saka a gaba, Soyayyar da nake miki ta yan uwantaka ce babu batun aure, wannan auren ki dauke shi bisa kaddran aka yi shi. Amma Lucky ita ce Zabina ban gaya miki haka don nayi hurt ɗinki ba, na gaya miki gaskiya ne domin ni bana cikin mutane masu son kansu ba, ba zan rabaki da kimar ki ba, bayan nasan ba sonki nake ba, kuma babu al'amarin soyayya da aure a tsakanin mu. Kin gane shi batu Sex and Romance scene kowa yayi fama da matsalar sa. Kin fahimta..... (Sorry mura ya saka ni a gaba ayi maneji) 08130269641 [17/06, 9:18 am] usmanlauratu71: 40... D'ago kai tayi tana kallon shi idanunta cike da kwalla da mamaki. "Hamma!" "Kin ga gaskiya na gaya miki, zan iya amsar wani abu daga gare ki, ki gane haka sonkai ne" ya fada bayan ya tawo gabanta ya durkusa. Goge mata kwalla yayi ya ce. "Ina son ki sani koda Mansurah ce a raye na hadu da Lucky haka ce zata faru. Dole zan iya tauye ta, shi yasa nake son mu fahimci juna sai a zauna lafiya. Nace ina sonki bayan ba sonki nake ba, akwai rashin adalci a cikin wannan yanayin. Please ki fahimce ni, don Allah" "yaushe zaka so ni?"mikewa yayi ya zuba hannunsa a cikin aljuhun wandon shi. Lashe bakin shi yayi tare da ciro hannu daya daga aljuhun wandon ya shafa kansa, "ki gane babu wannan zancen you're like my sister. Jeki kwanta sai da safe." Ya juya abinsa yana kallon wayar shi. Washi gari da safe, me aikin gidan su Latifah ta kawo musu abin karyawa, koda ta shigo hango Abaturab tayi yana ta shirya table. "Ina kwana Prince" "hey Helin ya aiki" "lafiya lau,abin karyawa na kawo muku" "thank you gashi nima kuma na mana, ok ajiye maybe Dr taci" "ok Sir" ta Ajiye. Ita kam burgeta yake yi babu ruwan shi, bai da girman kai sai ma girmama na gaba da shi daa ce wani ne da tuni an cika gidan da ma'aikata kamar me. Amma shi wannan da kansa yake girka musu abincin da zasu ci. Haka ta fita tana mamakin halin sa. Yana gamawa yayi wanka, sannan ya shirya bayan ya gama duba project din da da zai yi submit baki daya hankalin shi baya kan kome sai wannan aikin. A hankali ya fito kamar baya son fito ko ya tashe ta. Yana fitowa falon ya cire takarda da biro ya ce mata. "Ki karya ga wanda nayi ga kuma wanda Aunty ta turo ki kula da kanki sai na dawo" ya ajiye yayi fitar shi, sai wurin karfe goma ta farka , wanka tayi ta sauko kasa, duba kayan abincin tayi ta ga sakon shi. Murmushi tayi, a hankali abin da ya faru jiya ya dawo mata, a sanyayye ta zauna tana kallon abinciin. Kafin ta fara kokarin diban na shi, taci sosai sannan ta duba na gidan su farfesu ci ta mai da kome frij ta rufe. Komawa falo tayi ta ga ya gyara ko ina, komawa sama tayi ta gyara ɗakinta. Koda ta leka dakin shi, wani hoto ne babba a gefen gadon, sa'ade ce sanye da Uniform check pink Mr dara-dara. Tana murmushi lokacin tana Jss 1 aka yi hoton. A kasar hoton taga anyi karamin rubutu. Kamar haka ```Every moment of the day every minute in the time I think of you every while, since you have left me I have lost my smile I am missing you so today I am thinking of you I am so in love with you!``` Yours ............ AA sulu gambari. Cizon lips dinta tayi Idanunta yana cika da kwalla, tabbas kowani mutum da irin jarabawar sa, ita soyayyar Abuturab ita ce jarabawar ta. Anya kuwa? Wani bangare na zuciyarta ya tambaye ta, wani irin zaro idanu tayi waje, sannan ta ce a fili. "Kamar ya anya kuwa? Ina son shi mana" rintsa idanun tayi domin bata jin haka a ranta bakinta ne kawai son yake ajiye, amma a zuciyar ta babu zancen soyayya asalima, wani abu na daban ne. "A'a kare shi zan yi da rayuwata" ta fada tana zama a bakin gadon shi. Kuka ne ya kwace mata sosai take kukan ya gaya mata gaskiya amma me yasa ita ba zata gaya mishi gaskiya ba da abin da ta sani ba? Bai boye mata kome ba, amma ita ta boye mishi sakamakon mutuwar yan uwansa, me yasa tayi haka? Me yasa ta boye mishi gaskiyar da ya dace ace ya sani. ----- fitar shi daga gidan ya kira Ummi. "First love ya kike?" "Wa'alaikumunsalam" ta ce mishi. "Sorry Assalamu alaikum Barka da asuba" "da fatan ka tashi lafiya. ?" "Alhamdulillahi Ummina. Ya Yarana da Mama's dinsu?" "Suna lafiya, ina Y'ata?" Shafa kansa yayi sannan ya ce mata"tana lafiya na barta tana barci." Ya fada a sanyayye. "Ok ka kula da kanka sannan ka kula da ita." "In Sha Allah" daga haka suka yi sallama. Number Nazifi ya nima. Bayan sun gaisa ne yake tambayar shi Sa'ade. Yau kam Nazifi ya shirya duk abin da zai faru sai dai ya faru, kusan shekara kenan da auren Sa'ade bai san yadda zai dauka ba. "Nazifi kana jina kuwa?" "Eh Yallabai, dama ina ta son gaya maka an yi mata aure fa, kusan shekara guda kenan." "Lucky din ce aka mata aure?" Ya fada Idanun sa a warwaje. "Eh yallabai kasan halin malam Aminu wallahi kusan sayar da ita yayi." "How dare zasu mata aure bayan akwai baikona akanta?" " Da gaske abin da kowa yake fada kenan, kayi hakuri" "na gode " daga haka ya kashe wayar, wato shi da aka yi ta saka auren shi ana d'agawa, kafin aka yi. Kamar zai kira Ummi ya gaya mata, sai ya ga babu amfanin ya gaya mata, murmushi yayi yana shafa kansa. Ya ce . "Wanda ya auri lucky bai min adalci ba, domin nasan tana jira na" daga haka ya wuce ya cigaba da abin da yake. Domin baya jin kome da aka ce mishi tayi aure, yasan halin Kurman mutum da rike amana, don haka ya ajiye a ransa matukar rabonsa ce zata dawo gare shi yayi imani da haka. Har ya gama aikinsa ya nufi coffee shop din su, yana zuwa ya ga babu kowa a waje don haka ya saka kai zai shiga bayan ya bude kofar, sai ji yayi sun bude kwalbar barasa sun ce mishi. "Hurry!!!!!!!!!!" Wall na shagon an rubuta congratulations on your wedding day!. Murmushi yayi. "Thank you so much, amma kusan bana tu'ammali da barasa, na gode da karramawa." Anan manager din ya ce musu. "Yau za sha coffee kyauta, domin taya shi murnar auren shi." "Yeeeee mun gode" daga haka aka.yi ta rabon coffee da snacks. *** Toronto.Canada Yau kwana sati biyu kenan da zuwan su, amma bata tab'a leka ko waje ba. Tunda suka zo ba zata ce ta samu damar ganin masu gidan sai dare, daga nan kuma Abdul zai shigo dakinta yace zai wani abu da ita, karshe sai dai ta gudu ban daki. Kuma ya kwashe key din dakin. Sai taji alamar babu kowa a gidan, take fitowa ta saka kayanta ta fito niman abinci. Tana gamawa ta zauna a falon ta ci kaɗan ta dauki sauran ta koma dakin, a hankali take niman key din dakin, dakyar ta samo na dakin ta, sannan ta shige tana rufe kofar kamar wacce aka gaya mata ta bar key din a jikin kofar, rana yana yi ta fito ta yi abin da zata ci ta koma dakin ta rufe dakin har dare tana zaune. Kamar an ce ta duba kofar ta ga ana murd'a hannun kofar, tasan shi ne, tana kallon yadda yake ta kokarin bude kofar. Fir taki bude kofar yaji haushi ya kwaso jarabararsa, karshe dakin su ya koma da matar shi suka turmushe juna. Washi gari da gayya ya kwashe kayan abinciin gidan, dake yasan Sophia tana riga shi fita, sai ya tattara kome ya saka a dakin su, ya kama hanya ya tafi abin sa. Wani abin da bai sani ba, abincin da suka zo da shi daren jiya akwai sauran a firij, da suka watse ta fito ta duba babu kayan abinciin, yadda fuskarta ya nuna damuwa da sarewa zai baka tausayi. Kamar an ce ta bude firji din ta ga pizza da cake da ice cream, sai sai taliya. Dukkan ta fito da su ta dumamma ta kwashe ta kai daki, sanin cewa zai iya cire key din firji ta dauke key daya, kitchen din ma key din sa daya ta ɗauka. Ta nufi ɗakinta ta zauna tana ci tana kuka. Ita gida kawai take so, saboda ta ki amsar soyayyar ta shi ne baki daya ya takura mata yadda zata amince da soyayyar shi. Tayi kuka sosai har ta ji ta tsani kanta, baki daya ta rasa waye mai laifin jefata cikin wannan yanayin.. koda suka dawo bai wani bi ta kanta ba, sai can dare ya zo bakin kofar ya buga kofar yana rufe da alamun ma barci take ma, takaici yasa shi komawa dakin shi. Ya kudiri aniyar gobe ba zai tafi aiki ba, sai jibi. Haka ya kwanta da alkawarin gobe zai sauke kwadayin da yake cike da maran sa. Washi gari kuwa Sophia ta fita abinta. Sai da ta gyara ɗakinta sannan ta fito, da kayan jiya ta nufi kitchen ta fara kokarin duba abinci. Yarrrrr taji tsigar jikin ta ya mike, a hankali ta juya ya zuba mata idanu. Daga shi sai boxes. Sake plat din hannunta tayi tare da ja da baya, jikinta sai rawa yake, a hankali ya isa kitchen din. Ya rufe kofar yana murmushi. Gadangadan yayi kanta, cikin zafin nama ya cafketa, kuka ta saka tare da ture shi. Amma ina wani irin riko yayi mata, tare da hada ta da bangon kitchen din ya shiga lugwaigwaita yan matasa ta, ta fara kokarin kwace kanta, amma ina, ganin taki tsayuwa yasa ya jata suka fito waje, ya wuce da ita dakinsu. Anan Labarin ya fara sauya salo, domin da karfin gaske yake son dasawa kansa tubalin girma, amma ina karfi ne da ita kamar shara'a. Abin ta bashi haushi da mamaki, don haka ya shake wuyarta, sai kokarin cire hannun shi take amma ina. D'aga rigar jikinta yayi, ya saka gwiwar shi a tsakanin cinyoyinta ya bude yadda zai samu biyan buƙatar shi, ganin yana shirin rabata da rayuwarta. Kawai ta dunkule hannunta ta zuba mishi naushi a daidai inda aka mishi aikin zuciyar shi. Wani irin tsayawa yayi cak.... Happy weekend 😬 yarinya ta karasa gawar da ba nata ba, 😂🤣 Wallahi hukuncin kisa ya hau kan wata Y'a......[18/06, 8:00 pm] usmanlauratu71: 41.... Ba lallai kome kake so zaka samu ba, wani zaka duba kaga yadda kake ka fishi ta hanyar lafiya, arzikn, ƙwanciyar hankali da kome na rayuwa wani yafika ta kafi wani.... Alhamdulillahi Dafe kirjin yayi yana jan numfashi amma ina baki daya numfashin ya dauke wuta, so yake lallai ya ja shi baki daya ya kasa, haka ya fadi akan fuskar shi. Anan yayi ta shure shure, har ya daina motsi amma ba mutuwa yayi ba, ita kuwa tana samun damar fita, ɗakinta ta shige tare da rufe kofar. Tare da kashe wutar dakin ta makale can kuryan dakin jikinta sai bala'in rawa yake, domin bata taɓa shiga irin wannan yanayin ba, dukka-dukka shekarun ta, 15, ba wani abu bane yake saka ake kallonta sai girman kashi, da kuma tsawon kafa,amma babu shekarun. Wani irin kuka ne ya kwace mata, ga azzababen tsoron da ya cika ranta, gani take ya mutu, ta kashe shi. Kuka take har dare wunin ranar bata saka kome a bakinta ba, sai da garin yayi duhu. Karfe biyar Sophia ta dawo daga aiki. Tayi mamakin ganin kofar gidan a bude kenan Abdul bai fita aiki ba? Me ya faru, tana shiga kofar kitchen ta gani a bude, ganin shi kwance daga shi sai boxes yasa ta, shiga kitchen da sauri. Tashin hankali wayar hannunta ta fara kokarin kiran number gaggawa na asibiti, suna zuwa aka kira yan sanda, a binciken shi da waye a gidan yasa aka gano su biyu ne, don haka aka balla kofar, aka fitar da ita zuwa office din yan sanda, abin tausayi tsoro da firgici yasa ko kuka bata iyawa, sai zare idanu. An kuma rasa yadda zasu tambaye ta, an saka ta a cell kanta a cikin gwiwar ta, dole aka tura office din jakadanci da yake nan Toronto, aka samu bayanan Abdul Hakim Sharif Hamidu, daga nan aka tuntube office Shugaban kasar Nijeriya. Duk da shi Abdul Hakim din da sauki sai dai zuciyar shi da ta buga sosai. Dama kuma manejin zuciyar yake, daga can gida Nigeria aka sanar da Dr Sharif. ----- tashin hankali ba a saka miki rana, domin kuwa Hajiya Daula bata dauki al'amarin da sauki ba, sai da ta fara zuwa Maikulki ta saka aka kama Malam Aminu., Akan idanun Mai gari, yaso su sassanta amma matar nan taki. "Amma hajiya kin san dai ko ban haife ki ba, na girme ki ko? Ki tsaya muyi magana." "Wani magana zan yi? Wacce irin magana zan yi daku? Bayan Yar shi ta kashe min D'a? Dama ya aura mishi ita ne domin su ci gado ko? Tow wallahi karyanku ta sha karya sai an kashe shegiyar yarsa." "Innalilahi wa'inna laihil raju'un, Sa'adatun ce zata kashe Abdulhakimu? Haba dai ki sake sai ba zata kashe shi ba" "dattijo ina ganin girman furfuranka, bamu hanya mu wuce" "Malam Aminu kaga abin da ake gudu ko? Hakkin yaron can ne ya kama ka, Allah ya wanke Sa'ade." "Amin Ya Allah" mutanen wurin suka ce, ana tafiya da shi Inna ta fito zata bi bayansu. Ita kan bata san abin sa ya faru ba. Amma yadda mutane ke mata jajje yasa jikinta ya bata something happens kuma ana boye mata, Bashir dan gidan Uwar gidan mai gari ya dauke ta a mota, suka nufi bayan motar Hajiya Daulah da yan sanda, har Sokoto. Kafin su isa sokoton sai da suka tsaya a Binji aka ɗauki Ibrahim. Suka tafi state Cid. Abin tausayi sai da matar nan ta saka aka wulakanta Malam Aminu kuma aka hana kowa ganin sa. Duk inda suke tsammanin zasu ga Malam Aminu sun bi amma Hajiya Daulah ta sayi yansanda. Har dare suna bakin CID din, Nazifi yazo. "Ya ake ciki Ya Bashir?" "Gamu nan dai muna ta kokarin a samu ganin sa." "Tow ya labarin Sa'aden " kallon shi suka yi daga Bashir har Zakaria domin basu son Inna tasan halin da take ciki. "Muna kokarin mu anan" suka juya mishi harshen turanci, shiru yayi yana tausayawa Sa'ade. Fita yayi ya bar Office din ya kira Abuturab."yallabai akwai matsala da." Nan ya shiga bashi labarin abin da ya faru. Kafin ya kashe wayar. *** UK..... Shiru Abuturab yayi, yana kallon wayar shi kamar anan zai hango Sa'aden ya rasa meke damun shi. Dole yana niman izinin tsaya mata. Kiran Ummi yayi ya gaya mata halin da ake ciki. Shiru tayi kafin ta ce mishi. "Muna bukatar taimakon Waziri Dawood domin shi zai maka wannan aikin!" "Ummi ba ya mutu ba?" "Eh haka aka ce, amma a zahirin gaskiya Waziri Dawood yana raye, jami'ar Harvard na kasar Amurka." "Ummi ayi wani abu! Domin akwai case ne babba a gabana!" "Ok dole ka shigar da bukatar ka kungiyar Bar na nan UK, sai ka sake turawa izuwa na nigeria. Idan ka samu na nan UK zan gayawa Dawood sai ya san abin yi. But case din waye haka?" "Ummina!" Ya kira sunan a shagwab'e. "Na'am Assadullah" "ki min addu'a Allah ya bani nasara kawai" "ok ba za a gaya min gaskiya ba kenan?" "Zan gaya miki in sha Allah idan aka yi nasara" "Allah ya baka nasara" "Allahumma Amin, Ummulkhair" "na gode Assadullah" daga nan ya fita, dake a makaranta yake. Ya nufi department na Law. Nan ya shigar da bukatar shi, suka mishi alkawarin zasu tura mishi sako ta e-mail. Daga nan ya koma class ya hada kayansa ya nufi gida, kawai Addu'a da tasbi da haila yake dawaniya da shi, amma wallahi ji yake kamar ruhinsa aka rufe a can Canada. Kawai karfin hali yake amma tabbas ji yake kamar ya cire zuciyar sa ya huta. Koda ya koma gida Latifah bata fahimci yana cikin damuwa ba, sai dai ta lura yadda yayi keeping kansa busy. Amma ta ja bakinta tayi shiru, domin tasan bai zama dole ya gaya mata abin da yake faruwa ba, tunda su ahlin gidan sarauta haka suke basu cika bayyana damuwar su ba, domin kar a samu makamin da za a yake su. Don haka ta rufawa kanta asiri. The next day tana ganin shi dauke da manya-manyan takardun na Shari'a, a ranta ta ce . "Ko a ina ya fara aikin?" Kiran wayar shi aka yi ya dauka, daga yadda yake magana ciki -ciki zai saka ka fahimci wani abu ne mara daɗi, wanda kuwa ba wani abu ba ne, kawai gaya mishi da Waziri Dawood yayi ya tura babbab Dansa Ra'is ya isa Canada yasa shi jin kamar ya rufe Waziri Dawood da duka yasan waye Ra'is mayyen mata ne, dama yaya lafiyar kura balle tayi Hauka. Don haka bai sake Wazir ya gama magana ba, ya kashe ya wani kwabe fuska very annoyed ya kira Ummi. "Ummi me0 yasa waziri zai tura that pervert nan? Bayan kowa yasan his addicted on womenizer!" "Ubana Mangofak ya ci kaniyar sa, nace ka dauki icce ka rufe ni da duka, Are out of yourself ko? Wace ce yarinyar da ka dauki case ɗin? Kasan case din kisa kake son holding dinsa?" Kamar ya fasa ihu ya ce . "Ummi Lucky ce fa!" Daga haka ya kashe wayar. Kiran wayar sa tayi. "Auta taya akayi haka ya faru?" "Ummina auren dole suka mata" ya fada a shagwab'e, "kuma shi ne baka gaya min ba tuntuni " "tow Ummina ya zan yi?" "Ya zaka yi ka ce min fa? Dama iyayenta basu san da kai ba ne?" Kamar yana gaban ta ya ce Ummina ni kawai biyan kudi nayi a matsayin na saye...." "Kaniyarka da biyan kudi kayi da sunan ka saye ta. Aliyu me yasa baka kyautawa ne? Taya zaka biya kudi da sunan ka saye dan mutum?" "Ummina ai Babanta ne ya cika son abin" "yaushe ka fara blaming rayuwar wasu? Shi ne jarabawar Yaransa, kar na kuma jin kace ya cika son abin duniya, kayi kokarin kyautatta mishi Indai da gaske kana son Lucky haka, ka tsaya mata Allah ya maka albarka, ya jikan yan uwanka. Ka tsaya mata Allah ya baku nasara " da dukkan zuciyarta take bashi support. Tun daga lokacin ya kuma zage damtse wurin niman a kira shi Bar, Allah cikin ikon sa a cikin abin da bai wuce kwana biyu ba suka kira shi. Tare da bashi damar a rantsa da shi, duk wani shige da fecce Baban Latifah ya tsaya mishi. Duk da haka bai tsaya ba sai da ya kira Ra'is. Yadda ta gaya mishi al'amarin ya wuce tunaninsa kuma a haka wai yana bakin kokarin sa ne. *** A can Canada kuwa, kwana biyu da faruwan al'amarin Hajiya Daulah ta sauka bata jira Mijinta ba, domin yace mata zai tafi ya tattauna da iyayen Sa'ade. Amma ta ce ba zata jira shi ba, D'anta yana cikin wani mugun hali a ce ta jira. Dake ta san abin da ta shuka, kai tsaye asibitin ta fara sauka anan ta gan halin da yake ciki, hankalin ya masifar tashi, tabbas idan ta ga Sa'ade sai taci kwal ubanta, dole ta kare rayuwarta a gidan kaso matukar tana raye a nan Sa'ade zata kare rayuwarta, sai ta ga Gatan Sa'ade.....(Sannun ku ko ayi hakuri ba yad'awa)08130269641 [19/06, 8:48 am] usmanlauratu71: 42..... Da gasken gaske so take taga gatanta. Don Allah Sophia na zuwa ta balbale ta da masifa. "Kina ina tayi attempting kashe shi?" "Hajiya aiki fa na tafi, kuma taya zan sani" "Aikin ta ci kaniyar ta kin ji, mara kunya kawai wallahi kin yi sa'a saboda Hajiya Nazirah zan kyale ki amma da sai na daure har ke, a wani police station take?" "Ta nan kusa ne" "me kuka yi domin case ɗin?" "Kawai mun yi report ne da tayi yunkurin kashe shi." Gyada kai tayi kamar kadangariya, ta wuce gaba ita kuma tana bin bayanta, sai zagenta take a ranta. Har suka bakin asibitin suka tsari abin hawa in da ya kai su station. Lokacin da aka fito da Sa'ade ta fita hayacinta. Cikin fushi Hajiya Daulah ta tsinka mata mari, tana faɗin. "In sha Allah anan zaki tabbata, shegiya ba banza Allah ya barki babu gata da galihu ba, shima Ubanki na saka an tsare min shi, naga gatar ku." "Madam doka ta hana a tab'a lafiyar wanda ake tuhuma. Sannan kuskure ne a rike me laifi na tsawon awani 24 , ba tare da an mika shi ga kotu ba, akwai cin zarafi anan." "Waye kai?" Ta juya ga Ra'is, "Ni!" Ya nuna kansa, "ubanka na ke tambaya d'ana ta yi yunkurin kashewa fa! Don ubanka ka kawo min zancen banza" murmusa mata yayi ya ja kujera ya zauna yana kallon ta. "Ni suna na Ra'is Dawood Wazir, prosecutor din ta, kafin lawyer ɗinta yazo." "Kasan ni wace ce?" Ta fada irin cikin izgilanci!, "A'a Hajiya baki gaya min ba taya zan san ke wace ce? Ni ba wannan ba, nazo niman belinta ne fa" "na ga shegen da zai baku belinta wallahi sai kun san wace ce ni " "Ina ruwana da sanin Who are you. Belinta kan dole samu idan kin matso a karba miki hakkin ku, mu haɗu a kotu" "Yaro ka cire kanka" "Babu cire kaina da zan yi tunda akwai mahaukata dayawa a duniya d'anki yana can kwance kin zo kina son ki ci zarafin yarinyar da babu ruwanta." "Wallahi sai naga gatan ta." "Kaya da dai kince sai kin tsaya shari'ar da za a kwata miki hakkin ku, amma ganin gatar wannan yarinya babban al'amari ne" ganin zata tashi hankalin mutane yasa aka turo ta waje, shi kuma Ra'is ya samu ganin babban ispetor na Office, anan suka gaya mishi gaskiya ba zasu bashi ita ba, domin babu inda zata zauna kafin a shiga kotu, domin kar a bada belinta ta gudu, wannan al'amarin bei masa dadi ba. Don haka ya kira Abuturab ya gaya mishi halin da ake ciki. Shima abin da ya tsayar da shi har lokacin Nigeria ba ayi approve din shi ba ne,Five days da faruwan al'amarin cikin ikon Allah kuwa da Waziri Dawood ya saka baki, sai gashi ya samu approved, the next six days ya samu damar zuwa. Kafin yazo dole ya samu damar ganin Embassy na Nigeria dake mutumin bayarabe ne, daga Ibadan. A can Nijeriya aka yi connect din al'amarin, inda Ummi ta kira Uwargidan Alfe of oyo, ta gaya mata halin da ake ciki, kasancewar Matar jakadan gimbiya ce daga masarautar Alfe of oyo, ta kuma bukaci su taimaka mata. Cikin girmamawa matar da ta girmi ummi ta ce mata. "Duk abin da kike bukata zan iya kuma zan saka in-law dina ya miki. Don Allah yanzu zan gayawa Alfe ya shiga al'amarin." "Na gode sosai, Allah ya ba ni damar rama miki abin da kika min ." "It's my pleasure ko baki rama min ba, haka ya min tun da kakannin ku sun bamu damar cigaba da mulkin mu bisa ka'ida iya wannan ma ya ishe mu domin bamu da abin da zamu yi repayment din sa. " Ummi taji dadi don haka ta kira Abuturab ta gaya mishi zai sauka a gidan Jakadar Nigeria Dr Fayemi Jamil Adebayo. Kuma dake mutum ne mai ladabi da girmama na gaba da shi, take ya amsa ya kuma tsayawa Abuturab. Ko da jirgin su ya sauka, da motar office din jakadanci aka zo daukarsa, domin tunda Alafe ya gaya mishi Crown princes na kwara yazo akan case din da ake tuhumar wata yarinya yasa shi jin lallai case din babba ne, don haka a kan lokaci aka tsayar da zancen tare da nimo manyan lauyoyin kare hakkin dan Adam, aka saka su taya Abuturab da shara'a. Gidan jakadan ya fara sauka, tare da sakawa aka nimo mishi Ra'is domin yana ji a jikinsa dan iska yana can yana karewa Lucky kallo . A can kuwa kamar ya sani, idan ya kawo mata abinci. Tsura mata idanu yake abin ka da wacce take cikin tashin hankali, rigar jikinta da suka yi kokuwa da Abdul Hakim gaban ya ɗan yage, kana iya hango tudun wadanta a wurin, shi dai Allah ya gani yana kaunar tudun wadan mata, domin idan mace bata da tudun wada gani yake kamar ai jinsinshi ne, bata san me yasa yake zuwa ba, amma tabbas yana da kirki. Wayar shi da tayi kara ne ya dauka. "Dan iska kana ina?" "Gani a wurin Sa'adatu. Abuturab na tuba na daina bin yan mata Allah yarinyar nan zata gusar da ƙishirwa na, don Allah ka saka baki a bani ita" "zanci Ubanka, wallahi sai na saka an daure ka dan iska gani nan zuwa" aikuwa ko hutawa bai yi ba, idanun shi ta shiga hango mishi Ra'is ya matse ta, duk da shi kallon da yake mata, na yarinyar da ya bari ce yar kwailar nan da babu kome a kirjin ta. Haka ya nufi office din yan sanda, da takardun shaida inda zata zauna kafin a gama kome. Koda suka isa bai sake ya je wurin su ba, sai da suka fara hawa daga sama can, suka yi ta bata kashi da hujjar tsare ta da aka yi, tunda ɓangaren masu kara basu shiga kotu ba, shi zai maka su a kotu. Kafin aka bashi belinta ko abinci bai ci ba, daga wanka ya nufi office din. Tana zaune aka zo aka fitar da ita. Dake ya juya baya hannun shi a cikin aljuhunsa yana magana, ko a mafarki ba zata tab'a manta shi ba. Zubewa tayi a wurin. Tana kallon shi. "Sir she can walk" juyawa yayi ya kalle ta, gashin kanta yayi buzu buzu, gaban rigar ta a yage, cire top din kayan shi yayi ya nufe ta, tare da saka mata. Buge hannun sa tayi, ta kifa kanta a kafad'ar shi ta sake wani irin kuka. Janyo kanta yayi zai runguma. *Matar aure ce* cak ya tsaya yana jin kamar zuciyar shi zata buga aure ya musu iyaka. Kauda tunanin yayi ya d'ago ta, suka fita, rufe fuskar tayi domin hasken wajen don ciki babu hasken haka sai na lantarki. Kamar zata fadi haka ya rike kafad'ar ta, suka shiga mota. Amai ta shiga kwarawa. "Dan shegiya ya mata ciki" inji Ra'is, rintsa idanun Abuturab yayi, ga mace har mace amma gardin ya zuba mata kwallon a raga." Ya fada yana tsaki. Juyawa Abuturab yayi ya zuba mata ido, kwanciya tayi zazzaɓi na niman rufe ta. "Babu wani asibiti a nan kusa ne?" "Akwai wanda aka kwantar wancan dan shegiyar." "Ok muje " da gaggawa suka nufi asibitin da ita, karban su aka yi. Aka shiga bata kulawa. Sannan suka tura ta zuwa dakin da zata zauna, a can kuwa Hajiya Daula da D'anta an yi masa aikin gyara karfe ne tun kwanan ta hudu da zuwa, yau kwana biyu kenan da farkawar sa. Cikin gajiya ya ce mata. "Hajiya Ina yarinyar nan?" Wani banza kallo tayi masa. "Daga ita har ubanta suna hannun hukuma." "Me yasa zaki kai su ga hukuma?" "Domin tayi yunkurin kashe ka." "Hajiya ni na janyo haka fa" turo kofar dakin aka yi, Ra'is ne a gaba sai Abuturab a baya, kallon kallo suka farawa junan su, haka kawai Abdul yake jin haushin Abuturab, yayinda shi Abuturab baya jin haushinsa, sai ma yadda zai saka shi ya sake mishi Sa'ade. "Kai me ka kawo ka nan? Kasan wace ce ni?" Ra'is da ya gama bawa Abuturab labarin Hajiya Daulah. "As I said she's making me sick fa da gaya wace ce ita" lumshe idanun Abuturab yayi yana kallon magungunan Abdul. "Aliyu Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, AKA Abuturab lawyer din Sa'adatu Aminu Fulani." Ya d'ago kai ya zubawa Abdul idanu. "I know ka samu labarina." "Kai waye da zaka tsayawa mata ta." "Matar ka kace? Gaya min taya aka yi ta zama matar ka? Ta hanyar zuwa mutumin kauye kudi? Ko ta hanyar son kai? Ra'is bani takardar nan" Ciro wani takarda yayi daga briefcase dinshi, ya mikawa Abdul. "Ka duba ranar da na biya sadakin ta. Ranar da na ajiye shaidu akanta. Sannan yanzu zan shigar da karanku na yunkurin fyade da cin zarafi, sauran sai ta farka." Daga haka ya juya yana faɗin. "Yanzu asalin al'amarin zai so ma, domin a cikin tuhumar har da safara" daga haka ya juya zai fita. "Baka isa ba, Abuturab baka isa ba, wallahi baka isa rabani da Sa'adatu ba isa namiji muyi shara'ar a kotun Muslunci na Nijeriya" dariya Abuturab yayi ya ce. "Are you ready?" " Na shirya " "ai shi kenan " daga haka suka fita. "Kai ka sake masa ita" "wallahi gara na mutu ta min takaba da na sake ta" "zan tsine maka" "so what? Hajiya So what tsine min, ai duk abin da yake faruwa kusan tsinuwar ce, waye ya ce ki kaita hukuma kinsa waye wannan Yaron? Shi ya sota lokacin da babu me tunanin sonta, Hajiya idan kina son rayuwata ki dawo min da Sa'adatu haka zai saka na amince da ke uwa ce da tasan darajar D'anta." Daga haka ya juya baya. Abuturab kuwa, tsayawa yayi har dare sallah ma a dakin yayi, sai dare ya bar asibitin, washi gari yana zuwa ya samu ta farka, sanye take da kayan da ake sakawa marasa lafiya. Tayi rame sosai bakinta yayi fari, sai fuskar ta yayi pale, d'ago kai tayi ta kalle shi. Ganin abin sallah da mayafin da ya ajiye mata yasa shi fahimtar ta jima da farkawa, abincin da yazo da shi ya ajiye ya Ciro brush ya shiga ban daki ya kawo kwananon silver ya saka mata a gabanta, sannan ya latsa toothpaste ya mika mata, amsa tayi ta fara wanke bakinta tana kuka. Irin kuka mara sautin nan. Tana gama goge bakin ya mika mata goran ruwa ta kurkure bakinta, sannan ya dauki kome ya wuce da shi ban daki, sake hada mata ruwan zafi yayi, ya fito kallon ta yayi ya kalli banɗakin. Kanta a sunkuye ta mike tare da saka takalmi ta nufi ban dakin, duk wani abin da zata bukata ya zi mata da shi mika mata yayi, ta amsa. Ban dakin ta nufa, sai da tayi wanka sosai. Sannan ta fito jikinta har tana jin radadin sa, abinci ya jera mata. Ta zauna ta fara kokarin ci. Kallon ta yayi baki daya ta koma kamar bakuwa. A hankali ta fara cin abincin tana kuka. Murmushi yayi yana iya fahimtar kukan farin ciki ne, domin kukan babu hayaniya, tana yana kara mata, har sai da ta koshi. Ya tattara kayan abinciin da ta b'ata, sannan ya mai da su cikin kular. Mika mata takarda da biro yayi, d'ago kai tayi ya kalli takardan ya kalli cikin idanunta. Sai da suka magana ta Morse code sannan ta dauke kai, domin ba iya bayyana abin da yake bukata ba, wani irin abu take gani a cikin idanun shi. Samar takardan ya rubuta mata me ya faru? D'ago kai tayi ta kalle shi a sace, sannan ya fara rubutu, komawa daya daga cikin kujerun dakin yayi ya fara latsa waya kamar baya dakin, yana lura da yadda take kuka sosai, idan tayi rubutun sai ta share kwalla da bayan hannunta. Duk yadda aka yi wancan dan shegiyar ya cutar da yarinyar nan, ta shi yayi zai fita ta d'ago kai tare da marairaice fuskar ta.....08130269641 [19/06, 6:31 pm] usmanlauratu71: 43....Yadda take lashe pale lips dinta yasa shi jin like she driving him crazy, wani irin temper yake ji, na b'acin rai. Lumshe idanunsa yayi yana tambayar ta. "Kina bukatar wani abu ne?" "Karka tafi ka bar ni" ta sauka a gadon tana share hawayen da bayan hannunta, bayan shi ta nufa ta kifa kanta tana wani irin kuka me kashe jiki, a hankali ya ɗan matsa gaba. Sannan ya juya ya zuba mata idanu, had'e hannunta tayi tana rokon shi ka da ya tafi ya barta. "Bari na amso abu" ya nuna mata wuri ta zauna, sannan ya fita. A kan idanun Hajiya Daulah ya fita, da sauri ta shige dakin. Bata san ta shigo ba, sai ji tayi ta kamo kanta, tana gaura mata mari kau. "Shegiya karuwa dama abokin watsewar ki ne ya biyo ki" tai ta masifa tana marin ta, turo kofar aka yi, ita kan dake masifa ya ci ranta bata ma ji ba, ita wacce ake dukan ce take addu'a Ubangiji ya kawo Hammayo. Allah da ikon shi kuwa sai gashi sun shigo a tare da iyalan Ambassador. Tare da Ra'is a gefen su, "wai me yasa baki da girma ne? Baki san ina mutuntatta ki bane saboda mahaifiyata ba?" Abuturab ya fada bayan ya isa gabanta ya fisge kan Sa'aden a hannun Hajiya Daulah, da sauri Sa'ade ta shiga jikinsa tana wani irin kuka tare da rufe fuskar ta a kirjin shi. "A iya kokarina na lallai kar na gaya miki magana yasa naki kula yinki d'anki shi ne daidai dani amma baki fahimta ba, let me talk to you on harsh tongue kar na kuma ganin ki a nan idan ba haka ba zan saka a b'atar min da danki Billahi Azim mark my words" wani irin dauke wuta tayi. Kafin ta bude baki zata yi magaka Ra'is ya riga ta ce wa. "Kasan wace ce ita?" "Idan shi bai san waye ni ba kai kasan wace ce ni?" "Yunbu wacce idan ta mutu za a saka ta a ramin da za a saka talaka. Tsutsa da kasa suci kamar ta shi kenan ko na kara miki wace ce ke? Kin ga Hajiya Daulah Abdulhakim bamu bukatar sanin Who are you, kawai mu haɗu a kotu next month" Ra'is ya fada sannan ya wuce tare da ajiye basket. Kallonta Ambassador yayi sannan ya ce mata. "Sam Dr Sharif bai yi dacen mace ba wallahi mutumin kirki ya samu mahaukaciya!" "Hey kar ka gaya min magana." Kafin ta kara sa Ra'is ya ce ."ka san wace ce ita?" Ya fada bored face. "Mara kunya sai na daure ka" "Hajiya wai na gaya mishi abin da kike fada ne fa" shiru tayi babu shiri ta bar dakin, dakyar ya cire Sa'aden a jikinsa, wani irin kuka da tsoro ya kuma kamata, ta ki sake shi. "Ina ga ta razana ne, ka kyale ta zamu tafi kafin ku tafi dawo." Haka suka tafi suka bar shi da Ra'is. "Malam ka ce ta sake ka mana, she is my future wife." Tsaki Abuturab yayi yana zaunar da ita. Kamar zata shige jikinsa, domin wani irin tsoro ne ya kamata, domin gani take kamar zata dawo ta dake ta. "Turab ban gane ba, ka cire ta a jikinka mana" "kasan Allah, zanci Ubanka wallahi zan maka rashin mutunci bana son iskanci, she still teenage taya zan sake na baka aurenta dan ubanka." "Kai dai ka gaya min gaskiya kana sonta ne amma ban da cin baya irin ka me zaka yi da bazawara ka bar mana irin mu mana." "Kai dai anyi dan iska " "hoho duk abin da zaka fada matukar wancan tsohuwar tana raye a fadar kwara ba zaka auri bazawara ba banza kawai." "Ummina ce kawai zata ce min Asad ka hakura na hakura ko Dagus wallahi ba zan saurara ba, kai malam fita ka bani wuri kaje can kaci na turawa wannan matar aure ce " tsaki yayi ya fice, ganin babu kowa yasa shi bata rai ya janye jikinsa. "Ke matar aure ce, kuma baliga bai da ce muna samun body contacts ba kin ji " gyada mishi kai tayi Idanunta yana zubda kwalla. Komawa tayi can karshen gadon ta zauna. Tana me cusa kanta a tsakanin cinyoyinta. Har dare yana tare da ita kafin aka zo aka saka mata drip da alluran barci. Yana tsaye har barci ya dauke ta, dawowa waje yayi ya zauna, duk da an fara sanyi haka ya sa shi wucewa gida bayan ya bada umurnin a kula da ita don kar Hajiya Daulah ta kara yin nasarr cutar da ita. Washi gari kuwa yana zuwa ya samu har tayi wanka ta wanke bakinta, an kawo mara hot chocolate coffee da cookers mai daɗi. Tana ci tana idanunta yana kan door din. Ta keeping mind ɗinta da kome akan zuwan shi. Ai kuwa ya turo kofar dakin. Wani irin ajiyar zuciya ta sauke, tana wani narkan da fuskar cikin rigima da son kukan banza mara daɗi. D'aga mata gira yayi, ai kuwa sai ga hawaye sharrrrr. "Lucky rigima " ajiye warme din da ya kawo yayi ya ajiye ya fara ciro abinci, yana lura da ita yadda take niman rikici kin kulata yayi. Ai kuwa ta fashe da kuka, abinci ya zuba mata ya fara kokarin bata, aka turo kofar. Bai juya ba, "Kai dan iska kwarto ka bani mata ta." Juyawa yayi ya kalle shi. Sannan ya mika mata abinci. Ya koma kujeran dakin ya zauna yana me ciro wayar sa. Ita kan tun da ta ga Abdul tsoro yasa ta kasa cin abinci jikinta azzababen rawa yake, wani irin tsoro ya shige ta. Koda ya shigo har zuwa bakin gadon dira tayi tana niman hanyar shiga ban daki. Security suka shigo. "Malam zo ka fita" "ina zak tafi bayan ga mata ta anan!" "Ins shaidar da zai tabbatar da ita matar ka ce" wani irin crossing leg Abuturab yayi cikin wani bala'in izza yana me tab'e bakin sa. " Yayi mai wuri ya zo mai taburman ya nad'e " Abuturab ya fada yana jifarsa da wani banza kallo. "Kai ka isa na nime matar aure ne?" "Wacece matar auren? Auren dole ba kuma zaka sha mamaki domin sai na kure maka gudu " "idan ka isa Allah ya tsine min" "dama can tsinannen kake malam Lucky ta mai rabo ce " dakyar aka fitar da shi. Abincin da bata ci ba kenan. Ta nufe shi, Idanunta yana zubda kwalla. Yana sane da ita sarai yayi kamar hankalin shi yana kan waya, ea zata san yadda take haukata shi da kukan banza nan wallahi da ta rufawa kanta asiri ta daina kokarin zuwa gare shi, auren kanta ya mishi iyaka. Kuma a wannan yanayin ko karen haukace ta cije shi ba zai iya fito da zalamar shi na son ta ba, domin za a iya cewa ya kashe mata aure me ya aure ta. People of nowadays basu da gadonka amma suna da ta maganar ka. Buga kujeran tayi ta mika mishi takardan da ta rubuta mishi cewa. "Hammayo ka mai da ni wurin Inna don Allah " kalaman Hammayo ya mishi dadi, murmusa mata yayi ya ce mata. "Na zata baki kewar su ne yasa na bar ki ke zauna a asibitin." Ya rubuta mata. Da hannu ta cigaba da mishi bayanin don Allah ya mai da ita gida please. Murmushi yayi sannan ya ce mata. "Babu inda zan kai ki, gidan Mijinki zan kai ki" ya fadi haka ne amma kuma kalmar mijin ya bashi haushi wani mijin gare ta wanda a wuce shi? Amma kuma mata da miji sai Allah a banza sai ta iya cewa zata koma wurin wancan sakaran ko? Kamar tasan me yake tunani ta fara girgiza kai tana kuka sosai. "Don Allah kar ka kai ni, Baya bani abinci wai sai na yarda da soyayyar shi, Hammayo marina yayi na buge mishi kirjin sa, wallahi ban yi yunkurin kashe shi ba, Hammayo ka mai da ni gida." Idanun shi ne suka cika da kwalla. "Me yasa kika amince da auren shi ai kina son shi ne!" Hannu ya saka a wuyarta. "Na rantse da Allah bana son shi, na gaya maka,ba kai ne kace na jira ka ba" kura mata idanu yayi na few seconds kafin ya ce mata. "Kin jira ni ne" gyada kai tayi tana me ce wa. "Nace ba zan yarda da soyayyar shi ba, sai kazo shi ne ya je wurin Baffan mu, tun daga lokacin na tsane shi." "Idan na amince zaki zauna da shi?" Ya tambaye ta, turo kofar da aka yi yasa shi mikewa, yana kallon yadda kwalla suka bata mata fuska. "Ra'is yau zamu bar garin nan, zan sauke Lucky a Sokoto na shigar da karan wancan dan iskan" "wow Lucky da alamu Ni nayi Lucky." Banza ya bawa ajiyar Ra'is. Shi kuma ya cigaba da hada kayanta. Yana gamawa ya fito daga cikin dakin, yayi magana da daya daga cikin security din ,ya fita har shopping complex na asibitin ya sayo mata riga da facecap da riga me hula. Dawo mika mata yayi ta daura akan doguwar rigar ta.....08130269641 [20/06, 8:59 am] usmanlauratu71: 44..... Tana gama sakawa ya wuce gaba tana bayan da har suka bar asibitin gidan Jakadar Nigeria suka je, a can suka zauna kafin lokacin tafiyar su yayi, amma Abuturab yaga Jarabawa domin ko kwakwaran motsi Sa'ade ta hana shi, don dole ta zama tail din sa, ba don kome ba sai gani take kamar yana barin kusa da ita wani zai dauke ta ya mai da ita wurin Abdul. Haka suka wuni can la'asar jirginsu da zai kai su london suka samu, kiran Ummi yayi suka yi magana kafin ya ce mata. "Zan koma ga Yarki ta zame min tail" "Allah sarki, Abuturab ka ji tsoron Allah ka guji abin da zai saka ka kalle ta ta wani siffa na daban, matar wani ce don Allah kayi yaki da iblis ka dawo da ita lafiya. Don Allah kar ka sake duniya da abin cikin ta su rinjaye ka, idan baka ganin Allah tow shi yana ganinka, kar ka manta yayunka uku din matan aure ne, idan ka cutar da hijabin wani na yayunka mata bai tsira ba, na Future's children dinka basu tsira ba, ita din uwar wasu ce matar wani nace ba ka sani ba, ko da rabo a tsakanin su don Allah ka kiyayye idan ka kiyayye Allah zai kare naka ahalin please Abuturab " "in sha Allah Ummina zan yi yadda kika ce" "A'a ba ni nace ba, Allah da Manzonsa suka ce Ni yar tunatarwa ce." "In sha Allah, Ubangiji ya bani kariya daga kaidin shaidan." Sai da suka gama waya ya wuce gaba tana bayan sa, ya gama mata kome sannan suka zauna, yana kallon yadda ta koma tana kalle -kalle, har lokacin tafiyar su yayi suka wuce inda zasu shiga jirgi. Har suka shiga jirgi ya daura mata belt kalle -kalle take, lokacin da jirgin zai tashi sama ne ta diririce. Rike hannunta yayi yana girgiza mata kafi, tare da mata alamar ta rufe Idanunta. Haka kuwa tayi ta rufe Idanunta har jirgin ya daidaita nutsuwar sa a sama, sannan ya cilla da su. Cire hannunsa yayi akan nata, suna fara tafiyar barci yayi gaba da ita. Alqur'ani ya ciro ya fara karatu, lokaci zuwa lokaci yana kallonta har suka isa. Latifah ce ta zo ɗaukar su. Lokacin da ta gansu da sa'ade. Wani abu ne ya daketa. Domin ta wani fuskar kamar Ummu Mansurah, sai da suka iso wurinta, ta sake murmushi tana faɗin. "Welcome back" ta dan rungume shi, buga bayanta yayi. Sa'ade tana makale a bayansa. Murmushi yayiwa Sa'ade, tayi maza ta boye fuskartar a jikinsa. "Hamma ita wannan fa? Kasan suna kama da Ummu Mansurah a fisge." " Itace Lucky, zata huta anan kafin next week zata koma gida." "Hmmm!" Ta faɗa tana kara kallon Sa'ade yanzu don Allah wannan kwailarce yake ta ihun ba zai sota ba, don Allah dube ta fa yarinya kwaila da ita.(A'a Latifah rigar da ta saka ya boye Tudunwadar ta wallahi Sa'ade ba kwaila ba ce ahtoh kafin a Miki caaaa bari na gaya miki gaskiya akwai masu yin ta🧟🤣🙄😏) koda suka nufi wurin motar saka kayan su yayi sannan ya bude mata motar ta shiga, yana lura da ita tunda suka sauka take niman rigima. Share ta yayi ya rufe kofar, ya koma mazaunin drive Latifah ta koma gefen sa ta zauna, dawowa inda yake tayi ta kifa kanta a bayan sit dinsa. "Hamma amma wannan Lucky dinka shagwab'abiyya ce ko? Tunda na hango ku na karanci fuskar ta, tana son kuka." "Eh kin ga ni ai kema" leka fuskarta tayi suka yi idanu da Latifah ai kuwa ta fashe da kuka. Murmushi a ransa ya ce. *yarinya bari a raba ki da wancan dan iskan, zaki biyu sai na mai dake irina sak. Zaki gane alaka da auta irina ba sauki* (mun shiga 3 dama ya lafiyar kura 🙄 Joindah ji wani Iskanci wai zai koya mata mugun abu) haka suka isa har gida Latifah tana lura da shi yadda yake murmusawa which meant ya samu abin da yake so. Ita kuma ko oho, kishi da takaici yasata dauke kanta. Har suka isa gidan. Koda suka fito compound n gidan Sa'ade ta kalla ya mata kyau, amma tsoron kar abdul ya zo yasa ta komawa gefen Abuturab ya sakata a gaba har cikin gidan ya nuna mata ta bi bayan Latifah, dan guntun hawayenta ya fara matsewa, a take yayi Bala'in hade ransa, domin ta shiga hankalin ta, babu shiri ta bi bayan Latifah tana kuka, har dakin suka shiga ta ajiye kayan da Abuturab ya bata, ta nuna mata banɗaki. Sannan ta koma falo tana hada abincin. Wanka tayi da alola, tana cikin niman kayan da zata saka Latifah ta shigo. "Innalilahi wa'inna laihil raju'un" ta furta kamar zata yi kuka, yanzu da haka Abuturab zai shigo ya ganta. Gashin kanta wanda nature ne, ya sauka har kafad'arta. Tana daure da towel, iya gwiwar ta. Dan sunkuyawa tayi, domin idan ta sunkuya baki daya zaka iya ganin mazaunin ta, shi kansa towel din rike shi tayi gam, domin Tudunwada ya hana shi zama ta sama. Gashi wanke kanta da tayi gashin ya zuba sosai. A bayan ta da kafad'arta she looks beautiful sosai. Juyawa tayi ta fita a dakin, ta koma spare room da yake kusa da ita, sulallewa tayi ta zauna dabas ta sake wani irin kuka mara sauti, yanzu saboda ita Abuturab yaki amsar ta a mace? Saboda wannan yarinyar sai da ta sha kuka sosai, sannan ya mike ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta tare da duba kanta a mirror. D'ago rigarta tayi tana kallon kirjinta, taga ba laifi tana da Tudunwada nan dai itama, sai dai ita Sa'ade nata ya hadu da ganiyar balaga da kuma cikar budurci da kowacce mace take yi, shi yasa suke nan Masha Allah. Amma da zata kai ashirin da uku zasu dan ja baya. Haka yasa wasu masu hikima suke son auren karamar mace, domin daidai wannan lokacin ganiyar balaga da cikar budurci, mace tafi burgewa da haduwa. A can kuwa wani riga da skit yan kati da ya saya mata, sai wani hafvest da ta saka suka kara taimakawa kirjin mikewa tsam, ta saka rigar tana me komawa bakin gadon ta zauna, turo kofar aka yi Latifah ce. Wucewa tayi ta dauko handdry ta jona tana mika mata, akan ta busar da gashinta. Karba tayi tana kallo, dan turo kofar yayi yana faɗin. "Ku fito ina jiran ku ne, eh ki amsa ki mata mana, yarinya ce Maybe ma bata san yadda zata yi ba " "Amma dai ai mace ce!" "Karba ki mata as I say" "ok" karba tayi, ta fara kokarin busar da gashin ya juya ya fita. Yana ganin wani abu ya shiga kanta. Zama yayi ya kira Umminsa suka sha hira. kafin can suka fito. Mayafi ne a kanta domin Latifah kasa jure ganinta tayi a gabanta, shine ta bata veil. Yadda ta fito suka zauna ta fara cin abinci. Sai da suka gama ya koma falon ya kira Nazifi. Ya hada shi da Inna ya ce mishi ai tunda taji labarin abin da ya faru da Sa'ade bata da lafiya. "Zata iya magana." "Eh zata iya amma ba mai tsawo ba" "taimaka idan ka samu lokaci ka haɗa mu da ita" "in sha Allah Sir" daga nan ya kashe wayar, yana kallon ta tana zuba gyangyadi. "Ki tashe ta ta wuce daki" wani haɗe rai tayi iya ba zata iya bautar ta ba Allah ya gani. "Batar zan kaita" a tunanin ta daukar Sa'ade zai yi da sauri ta mike tare da tashin Sa'ade suka nufi cikin dakin. Barci sosai ya dauke ta tana ƙwanciyar. Tana fitowa ya tsare ta da idanu. "kayi hakuri" dauke kai yayi ya cigaba da abin da yake. "Amma kasan dole raina ya sosu, ita din yarinyar da kake so ce, ni kuma matar ka ce." D'ago kai yayi ya kure mata kallo kafin ya lashe baki yana kallon tv. "Idan wani ya ce min zaki iya cewa haka zan iya ƙaryata shi, amma da kika fada da bakinki na cewa ranki ya tabu na yi mamaki. Look ban kawo Lucky don na musguna miki ba, na kawo ta ne domin ta samu nutsuwa kafin na mai da ita wurin Iyayenta. Don" "daga ina ka dauko ta?" Sanin cewa tana da hakki na sanin kome ya sa shi gaya mata, batare da ya damu ba domin sam bai da tsoro a kanta ko fargaba. "matar aure ce wannan yar abin? Baki daya bata wuce sha shida ba" "bata kai ba, domin a 11yrs ta shiga secondary sector, yanzu tana 15yr da watanni ne tara, da sati biyu da kwana biyu." Sake baki Latifah tayi tana kallon shi. " Yaushe ka fara sanin." "Hmmm" ya ce mata yana kallon tv sam hankalin shi yana kan tv. Itama ganin yayi shiru yasa ta mai da idanun ta kan Tv. "I hope tai sallah?" "Eh tayi," "ok bari nima naje na kwanta" wucewa dakinsa yayi ya kwanta, tare da janyo pillow ya runguma. A can Canada kuwa, birkicewa Hajiya Daulah Abdul yayi shi matar sa zata dawo mishi da ita, karshe ya bar asibitin ba a sallame shi ba, a tunanin shi sun bar ƙasar. Don haka dan batalikin nan ya taso uwar a gaba da Sophia ta ce ba zata bisu ba, domin tana fama da aikinta. Haka suka tawo suka barta a can, kafin wani lokaci sun iso abuja. Daga can ne suka nufo sokoto. Koda suka iso kai tsaye office din yan sanda ta nufa tare da tambayar malam Aminu aka ce ai Mijinta ya saka hannu a nan sake shi. Kallonta Abdul yayi kamar zai rusa ihu, gidan Zakaria ya nufa. A kofar gidan ya ga Malam Aminu zaune shiru, yadda ya fige zaka fahimci yana cikin tashin hankali wani hali Sa'a take ciki. Tun tashin yarinyar bata da kuzari da ƙwanciyar hankali, ya hanata sakat abin da ya zaunar da shi a nan Husnah da Kubrah suka zo domin labarin abin da ya faru ya bazu har a makarantar sai da aka gaya musu, shine suka zo jin labarin ya Sa'aden hankalin Husnah ya tashi sosai. Domin wani irin kaunar Sa'aden take, kamar ciki daya suka fito. Dama Rahilah bata dawo ba, sai su kadai. Ko wancan hutun da suka samu sai da ta je gidan su Rahilah a nan ake gaya mata ai dan uwan Mamanta ya dauke ta, kuma ba a kasar zata zauna ba. Zai tafi da ita Cairo a can yake aiki. Tasha kuka sosai, itama Mahaifinta sun koma lagos da zama sun yi sunyi ta bisu akwai makarantar a can ta ce a'a su barta tana tausayin Kubrah ce idan ta tafi kuma tasan Sa'ade da Rahilah zasu iya zuwa nimanta. Dake iyayenta suna bala'in sonta yasa suka barta, bayan tafiyar su ne malam Aminu ya zauna shiru, musamman yadda yaga Husnah tana kuka sosai. Fitowa Abdul yayi ya nufe shi. "Baffan Sa'adatu" d'ago kai yayi, suka yi ido hudu da Abdul ya juya gabar ya juya yamma, wato da malam Aminu ya takarkware ya fasa ihu ya shiga cikin gidan yana me garkame kofar gidan "Baffan Sa'adatu ban mutu ba" "Wallahi karya kake fatalwa ne kai ka mutu uwarka ta gaya mana Sa'adena ta kashe don Allah ka koma kabarin ka, ka kwanta kowa haka yake rayuwa idan ya mutu hakura yake da rayuwar duniya ya rungume ta lahira" "Na rantse da Allah ban mutu ba," "dama waye zai yarda ya mutu? Bayan mutuwar karfi kayi bata a hankali ba, ka je Allah ya jikanka" "Na rantse ban mutu ba" "Allah sarki Fatalwa bata maka adalci ba laifina ne da na mata auren dole shi ne kazo daukar fansa kayi hakuri ka kyale Ni daga yau bani kuma yiwa auren dole, ka koma kabarin ka, ka kwanta Allahu ya jikanka yaron kirki me kyautar arzikn." (Jama'a Man Aminu bai nutsu da rayuwa ba har yau zancen arzikn na nan a ransa ina zai kai shanun sa nan?) 08130269641 [21/06, 7:34 am] usmanlauratu71: 45... Buga kofar da ake yasa Aunty Ummy fitowa daga dakinta, ganin Baffa a tsaye ya daddage ya rufe kofar gidan yasa ta ce. "Baffa lafiya?" "Ke koma cikin ɗakinki, ki kwanta fatalwa ce a kofar gidan ina budewa zata shigo ya hallaka ni" "Fatalwa a wannan era din?" Ta tambaye shi baki buɗe, "ke kiyi kasa da murya shiga daki kar ya shigo ya fara dake maza shige daki, dole yau mu ga bayan shi" yadda yake magana yana muzurai zaka rantse da Allah wani jarumi ne can, "Baffa na rantse da Allah ban mutu ba, ka bude min kofa na gaya maka Sa'aden Inna wani ya dauke ta." Cak ya tsaya tare da dan bude kofar ya leka yana faɗin. "Da gaske baka mutu ba?" "Wallahi ban mutu ba, Baffa waye Abuturab." Wani irin rufe kofar yayi kirib, "Baffa bude min!" " Me ya hada ka da shi? " "Ya dauke Sa'adatu" ya fada mishi cikin babbar murya, "shi kenan ai tunda ka sake ya dauke ta, ko dudduniya zasu taru ba zai baka ita ba, sannan bari na gaya maka ko dan abin da mahaifiyar ka tayi ba zama dole ya baka ita ba. " "Baffa mata ta ce?" "Ai babu wanda ya ce ba matar ka ba ce. " Ya fada bayan ya bude kofar gidan. "Babu wanda zai ce ba matar, ban sani ba ko Mahaifiyar ta da yan uwanta zasu yarda a dawo maka da ita amma abin da Mahaifayar ka tayi be zama dole a dawo maka da ita ba." Jikinsa har wani irin rawa yake ya ce. "saboda me yasa, ina son mata ta, kuma ni tayiwa laifi ba wani ba." Murmushi Baffan Sa'ade yayi ya ce mishi. "Kana sonta me yasa ka dage zaka aure ta, bayan kasan mahaifiyar ka bata kaunar talaka? Karin abin takaici marin Mahaifiyar Sa'ade tayi bayan ita bata yi mata kome ba, ni ya da ce ta mara. Me yasa? Me yasa? Me yasa na ce maka? Ka sani ko mutuwa zaka yi matukar Sa'adatu tana hannun shi ba zai tab'a jin tausayin ka ko ya baka ita ba, da ace hannun mu ta dawo tow da zamu iya baka matar ka amma ban da shi domin ka tako rigimar da baka da me tsaya maka sai Allah. Don ya dauki Innar Sa'adatu matsayin uwar shi" mikewa yayi yana faɗin. "Ko zan mutu ba zan tab'a bar mishi ita ba." "Allah ya baku sa'a" Baffan Sa'ade ya fada yana shiga cikin gidan. Gidan Aunty Fareedah ya nufa, tun daga bakin get aka ce ai Mahaifin shi ya hana ya shigar mishi gida, don haka ya juya tare da komawa gidan Hajiyar shi. Anan ya samu tashin hankali goma da Ashirin mahaifinsa ya sake ta. "Ka dai gani saboda ita wancan yar iskar yarinyar ya sake ni!" "Eh ya kyauta ai, waye bai san halinki ba, Hajiya marin mahaifiyar Sa'ade kika yi? Me ta miki? Hajiya me yasa da kika haife ni baki kashe ni ki huta ba? Bayan haifa na da kika yi da ciwon zuciya haka bai isa ki taya ni niman farin cikina ba? Hajiya tun tasowa ta ban san dadi da farincikin rayuwa ba, sai bakin ciki da sani abu dole. Hajiya kamar yadda bakin son Sa'adena haka mahaifiyar Sa'adena bata sona, amma ta danne zuciyarta tana saka ran zamu hade kan mu, kar ta tsannanta muzo mu hade kai ta ji kunya, Hajiya me yafi haka ciwo kasan danka bai son abu amma kuma ka saka shi dole yayi shi matar nan tayi, tana da ikon hana auren Amma tayi hakuri, daga ita har yarta ban tab'a basu kyauta sun amsa ba. Duk abin da kike zargi Uban Sa'adena ya amsa, Hajiya Abuturab ba zai tab'a bar min ita ba, matukar yana raye, haka kawai daga jin labari min bazama kin kama uban yarinya. Allah gara ba mutu da ina gani Sa'adena ta fita a hannuna " ya juya ya haura sama, tana jin shi yadda yake farfaasa kayan dakin. UK... Washi gari. Bayan sallah asuba, da kansa ya shiga kitchen ya daura abin karyawa. Yana cikin soya pancake, Latifah ta shigo kitchen ɗin, dan hug dinsa tayi tana faɗin. "Morning Hamma" "morning dear" ya cigaba da aikin sa. Yana gamawa ya shiga zuwa kome a cikin warme yana fita da su tana taimaka mishi. Yana gamawa ya wuce dakinsu yayi wanka, kafin ya fito ta cire mishi blue jeans and white shirt, yana fitowa ya saka, ya shirya sannan ya fito falo. "Ina Lucky?" "Tana fitowa domin naga tayi wanka." "Kira ta mana zan fita school ne, sai yaushe zaki tafi aiki" "Sai yamma" "ok" yana zaune ta fito sanye da riga da skit irin na jiya, domin kusan kala uku ne kayan. Sai mayafi da ta yanne kanta. Ta zauna ta fara kokarin gaishe, ya amsa sannan ta juya ga Latifah tayi kamar bata fahimci abin da take nufi ba. "tana gaishe ki ne fa!" "Ai" ta mata yake sannan ta fara cikin abincin, shi ya zuba mata da cup din tea don sangarta, kamar wata yarinya karama ya hada mata tea me kauri, sanan ya zuba mata farfesun kazar da yayi, ya tura mata. Murmushi tayi tana mishi godiya. A ransa ya ce. *Thank Goodness babu rikicin banza* haka taci kaɗan, tea ɗin take sha, tana lumshe idanun, ya mata dad'i. "Ya miki dadi ne?" Ya tambaye ta. "👌" Ta mishi haka da hannu tana murmushi. Murmushi yayi ya cigaba da cin abincin sa, can ya mike tare da zuwa ya dauki top ɗinsa, ya zo ya fada mata. "Zan tafi school " Idanunta ne yayi rau-rau alamar zata yi kuka. "Kiyi shiru zan dawo da wuri." Gyada kai tayi hawaye na zuba mata. "Hamma kasan dai matar aure ce." "Kin ga nayi wani abu ne bayan baya hakuri?" Ya tambaye ta, yana tsare ta da idanunsa masu shegen kaifi. "Allah ya baka hakuri, wai naga ta cika shagwab'a ne" "hmm" ya ce yana me barin gidan, ya tsani haka, ai kuwa bayan barin shi gidan Sa'ade tayi ta kuka tare da makalewa a jikin kofar fita. Takaici ya ishi Latifa, ta riko hannunta, ta mai da ita daki tana me zare mata idanu, babu shiri ya ja bargo ta kwanta. Dama Hajiya Daulah ta gama furgitatta. Haka ya tafi makaranta yana gama abin da zai yi ya kira Nazifi ya hda shi da Inna, sun jima suna magana, sannan ya gaya mata Sa'adenta tana wurin shi nan da sati biyu zasu zo yana son ta huta ne na kwana biyu sai tawo da ita. Ta saka mishi albarka ya fi sau goma, domin wata irin yarda take da shi akan sa, ta yarda da shi dari bisa dari. Haka suka yi sallama. Sai da ya biya ta shagon su. Sannan ya dawo gida, lokacin Latifah tana wurin iyayen ta. Bai ji dadin yadda ta bar Sa'aden a gida ba, amma sai ya share ya saka Sa'aden ta fito ya kawo ta ta gaida iyayen Latifah. Dake Baban Latifah ya san da zancen bai damu ba. Mamar ce tayi ta cika tana batsewa, daga nan ya dauki Sa'ade suka wuce kasuwar zamani yaje yayi ta kona kudi yana saya mata kaya, da tarkacen mata, bayan ya gama sayayyan ya wuce wurin sanitary pads, na kamfanin always ya saya mata. sannan ya saka mata a cikin kayanta bata sani ba. Idan har yadda yake tsammanin ne da yadda yake kallon ta, babu kome a tare da ita. Wani abin da bai sani ba, ita Sa'ade tana iya kure wata biyar bakwai bata yi period ba, kuma ba wani abu ba ne, kawai haka Allah yayi ta. Koda ya zo kwana biyar yake ya tafi, kwana uku yana zuba sosai na sauran biyun kadan har ya dauke, ita ko irin ciwon nan bata sani ba. Haka suka gama sayayya suka dawo, gidan a hanya ya ga teddy Riley ya saya mata, pink colour. Sai kallo take tana murmushi. "Na gode" ta mishi godiya, yana rike da kayan har suka dawo, ya dauka a daidai Latifah zata tafi aiki suka shigo gidan, kallon shi take, ita gwanar rike da dollin shi kuwa rike da kayanta niki-niki, gwanin ban sha'awa. Sai murmushi take, ta kuwa rike dolli kamar za a fisge mata shi. "Prince amma" zuba mata idanu yayi yana faɗin. "Yarinya ce bata da wayo da hankali. Idan na gama case ɗinta nan zata dawo ta karasa karatun ta." "Daga nan sai ku cigana da forbid affairs?" "Eh akwai abin da zaki yi ne?" Ya tambaye ta, kai tsaye tare da hade fuska. "Babu abin da zanyi ka fitar min da ita a gida!" "Gidan ki ko gidana? Gidan nan Sultan ya saye shi da sunan Yaran shi maza uku, sannan rabi na magadan Mazan ne sauran nawa ne, a ina aka saka sunan ki? Kin san dai abin kike ba zai tab'a sauyawa tuwo suna ba, sannan haka ba zai tab'a hana ni abin da nayi niyya ba, da ace ban gaya miki wace ce Lucky ba, zan karbi zancen ki amma kuskure ne babba niman dakatar da ni daga matar da nake shirin zama da ita har a gidan aljanna. Na ajiye kowacce buri domin ita ne, ko Mansurah ce a matsayin ki abin da zai faru kenan. Ita dai da muka taso tare muka girma tare, har aka kawo zancen aure a tsakanin mu, soyayyata daban zumuncina daban, bani hanya " ya wuce Sa'ade tana me bin bayan sa, dakin ya kai mata ya zuba a kan gado, sannan ya koma dakin sa, ya sauko mata akwati babba, ya zo ya zuba mata kayanta, duk abin da take bukata, sai da ya zuba mata. Abin da Latifah ta gaya mishi ya mishi ciwo, don haka ya share. Fitowa yayi ya Ciro kayan girki, ya leka dakin yaga Sa'ade rungume da dollinta, kiranta yayi ta fito rungume da teddy. Ya saka mata kujerar kitchen din ta zauna, ice cream ya bata. Sannan ya cigaba da aiki tana zaune har ya kusan karewa, ya mata magana suka fito,.alola yayi ya ce mata taje tayi sallah, masalaci ya fita, itama tayi nata a gidan. Yana dawowa ya samu ta idar gashi babu kowa sai zare idanu take, dariya ta bashi haka ya zubo mata abincin. Tuwon shinkafa miyar vegetables, da yaji kayan kamshi da nama hade da ganda. Zama tayi ta ci sosai. Har da gyada kai, domin ta jima bata ci abincin gida haka ba, ko zamanta a Sokoto ba wani abinci take ci ba, shinkafa ce dai ita kuma saurin hawa kai ta a'a, ita kuma Rahilah take musu kwad'on gaya, shi kenan ko tazo Hutu, Aunty Ummy tana tuwo da sauran cimma. Haka yasa tafi son sauran cimma sama da shinkafa, duk da tana so, amma mai da yaji ko da miya. Sai da tayi nisa a cikin ne ya tuna da manshanu ya kawo mata, da yajin daddawa. Murmushi tayi tana ci yana mata hira. Har ta gama ta kai plat din kitchen ta wanke, shi kan gwanin tsafta ya gyara ko ina abinsa. Tana gamawa ta dawo falon, lokacin Isha yana yi ya tafi sallah itama tayi a gida, koda ya dawo barci ya fara kokarin tafiya da ita, tashinta yayita wuce dakin Latifah. Latifah bata dawo ba sai da sassafe, yana kallon yadda take tafiya a gajiye, ya dauke kai. "Kayi hakuri da abin da ya faru?" Murmushi yayi mata yana faɗin. "Duk wanda ya zargi wani ba tare da yq kafa hujja hukuncin sa a musulunci bulala ne, and kuma Allah ya kyauta." Ya cigaba da aikin soya doya da kwai, sai kunun koko da zai yi na jar dawa, bai da mu da cimmar turawa ba, gida kawai yake sakawa a masa aiki, zaman shi a Maikulki ya saka mishi son cin tuwon gargajiya, koda ta shiga dakin ta, ta samu taba gyara gadon, koda ya ajiye kayan ta, tattara su tayi ta saka a saman mirror, ko da ta shiga ban daki sake baki tayi domin yadda aka wanke aka gyara kome sai ya burge ka, wato masu tsafta kome nasu daban yaƙe. 08130269641 [22/06, 5:19 pm] usmanlauratu71: 46.....Kasa hakuri tayi ta leko tana kallon yadda ta kara gyara dakin, komawa ban dakin tayi, tare da wanka sosai. Sannan ta fito lokacin Sa'ade bata dakin, ko da ta shirya ta fito waje, ta samu suna ta hira irin nasu, don haka tana fahimtar wasu abubuwan. Wasu kuma sun mata tsauri, zama tayi ta fara kokarin diban abincin bata damu da ko sun ci ba ko basu ba, burinta ta ci ta kwanta. "Ina son ganin likitan kunne ki nima mana appointments mana" bata kalle shi na ta ce mishi. "ok yaushe zaka kaita?" "Zuwa gobe." "Ok zan yi magana da Dr jin huk" daga haka suka cigaba da cin abincin. Wayar shi ce tayi kara ya duba number Nazifi ne, katse kiran yayi ya kira Nazifi. "Ya dai?" "Ina ce ta ce tana son jin ko da saukar numfashin Sa'ade ce, gani take kamar ka fada mata ne don hankalinta ya ƙwanta amma bata yarda Sa'ade tana tare da kai ba." murmushi yayi sannan ya ce. "kana tare da ita ne?" "Eh Allah ya baka nasara" kallon Sa'ade yayi sannan ya ce. "Bata wayar!" mika mata tayi yayi. "Innarmu ya jikinki?" Ta amsa da sauki. "Gadanga da gaske kana tare da ita?" "Innarmu kenan, bari na baki ita" mika mata wayar yayi ya mata alamar da hannu taja numfashin sama, sannan ta sauke a hankali. Hawaye ya zubo mata, a yau tayi bakincikin rashin bakinta yau tayi bakincikin da rashin yin magana kamar kowa. Tausayi ta bawa Latifah, a ranta ta ce. *Shegen gulma gara ki koma wurin mijinki ko na gane hankalin shi* a zahiri kuma ta tausaya mata so. Amsar wayar yayi, ta mike tare da barin wurin, yasan kuka take. Girgiza kai yayi ya saka wayar a kunnen shi. "Innarmu!" "Aliyu haidar" ta kira sunan shi. "Na'am Innata" ya amsa yana Mikewa domin yadda ta kira shi yasa shi fahimtar tana da magana me muhimmanci. "Ina son ka dawo min da ita ne, sannan ka min Alfarman ɗaya, ka kwatar mata hakkinta" "sai me kuma Innata" "sai ka nisantatta da Malam domin zai iya sayar da ita kuma domin kudi ya fi mishi kome" "Sai me kuma Innata" "Na baka ita duniya da lahira" baki daya ya rikice, ya rude ya rasa inda zai tsoma ransa, wani irin alamari yake ji, cikin dattako ya ce mata. "Innata!" Ya kira da serious tone, sannan ya fara magana a hankali a karan kansa yake son magana. "Innarmu, dole hakkinta sai kotu ce zata kwatar mata, zan dawo da ita gida kamar yadda kika ce, amma batun kin bar min ita be taso ba, tana da damar zabawa kanta abin da ya mata, ba dai a kara kwatanta irin na baya ba." Wani irin girmansa da kimar shi ce suka kara samun muhalli a Zuciyar ta, addu'a ta shiga zabga mishi tare da bashi sa'a, bayan sun yi sallama kenn ya juya zai koma cikin gidan idanu biyu yayi da Latifah jikinta yayi sanyi. "Yaushe kika fara labe?" "Tun lokacin da aka kira ka." "Kin kyauta kenan?" "Me yasa?" Mazgewa yayi ya ce mata. "What?" Ya wuce abin shi. "About your dream?" "Ho wanne kenan?" "Ka da ka manna min hauka mana" "oh sorry ban manna miki hauka is alright?" Ya dauki kayan shi zai fita ta ce mishi. "about Lucky?" Cak ya tsaya murmushi yayi ya cigaba da tafiya ya ce mata. "Kin ce baki son kishiya ni kuma bana son tension shi yasa na bar ta." "Hmmm yaushe ka fara karya?" Ta fada tana zama abinta. "Ban fara ba kuma ba zan fara ba, da gaske idan ina so ina so ne idan bana so ko kare ya fi shi daraja." "Shi ne kayi rejected ɗinta." Juyawa yayi yana kallon ta ya ce mata. "she just 15yrs bata san ciwon kanta ba, sannan a wannan lokacin aure ne a kanta, kika sani ko ciki ne da ita? Kin ga idan tana son mijinta fa? Look kakanni mu sun yi gaskiya da suka ce sirrin ciki sai hanji don haka a nima mata hakkinta ba kafin ba ne kuskuren shi ne ayi forcing dinta taso wani abu bayan zuciyarta yana wani wuri na daban, i know i like her but bana fatan ayi forcing dinta, so koda zan kare rayuwa a matsayin tuzuru mijin qanwarsa bana fatan nayi auren dole akan matar da nake so zan iya zama da macen da bana so, amma ba zan iya zama da macen da nake so a matsayin dole ba zaka iya hakuri ka amshi macen da baka ra'ayi, ba wai na gaya miki ki ji haushi ba ne, a'a iya gaskiyar kenan, macen da kake so bata sonka kamar gini ne bisa teku ai kin san ba sauki, domin ya zama kamar cin zaline, bye." Ya saka kai ya bar gidan, tunda ya fita ta zuwa kofar idanu, kamar tana jiran ya sake dawowa. Wani irin tausayi ya bata, yana son yarinyar amma ya cire son zuciyar shi domin kar a tauye ta shi kuma ya amshe ta saboda biyayya. Mutum ne shi mai gaskiya da amana, me hakuri da duk halin da yake ciki, don kar ya kasa adalci ya ki amincewa yayi rayuwar aure da ita. Wani lokaci har haushinsa take ji gata mace har mace, amma kuma baki daya sai take ganin kamar ta gaza ne yasa yake dauke kai, amma ganin yadda ya hakura da damar shi gaskiya shi na musamman ne, shi yasa ko jiya sai da Mahaifinta yayi mata fada, barinta ita daya a gida. Wanda kiri-kiri Uwarta ta nuna damuwarta akan me yasa take zaune da su, da ta dawo part din su, tunda ya iya kawo mace gida. Ai kuwa Uban ya ce mata. "kar ki sake ki shiga tsakanin su. Shi din fa Basarake ne wata rana, dabi'ar su ce tara mata. Don jin dadin su, don Allah idan ba kauce hanya yayi ba, babu ruwan ki akan matan da zai kawo." Ya musu tass, babu ruwan su da duk macen da ya kawo. Dake bata gaya musu asalin abun da yake faruwa ba, sannan ko da ace ta gaya musu gaskiya ba zasu wani damu ba, domin ta lura yadda ake lallaba Abuturab yasin ko Ubansa da yake Sarkin ba a lallaba shi ba. ---- A hanya ya kira Ra'is. "Hello kazo london nan da sati daya kai ne zaka tsaya mana." "Wayyo ina lucky?" "Kasan" "karka damu nasan wane ne kai! Don haka kawai ka mikawa Lucky sakon kiss dina, kafin na zo." "Idan mijin ta yaji abin da kake akan matar shi sai ya ci ubanka" "na gode " haka suka yi sallama. Sannan ya kashe wayar. *** Kwara. Gyara gashin kanta take gyarawa, idanunta yana kan madubi. Tana sama amma tana jin hayaniyar abin da yake faruwa a kasa, murmusawa tayi ta tattara gashin kanta, kamar wata yar shekaru talatin da biyar, babu ruwanta gashin kanta me cike da furfura bai hanata ta gyara shi tsaf kamar budurwa. "Ku kyale ni, don Allah ku bar ni ba tafi wurinta." Tun daga can take jin magiyar da Sarah take har suka hauro sama, turo kofar dakin suka yi baki daya. Bata fasa saka dan kunnen ta ba, ta zube akan gwiwar ta. "Queen Mother, kiyi blessing dina da auren Abuturab. Don Allah Ummi ki bar ni ba auri Ali shi ne dream dina." Tana hango yadda take kuka sosai. "kuje Zuwairah " Ummi ta fada tana saka zoben gold a yatsanta. "Na albarkace ki da auren Ali? A haka zan bari ki aure shi babu respect?" Wani irin kuka ta sake ta ce. "Queen Mother, zan gaya miki gaskiya. Abubuwan da na sani don Allah kar ki saka Abuturab ya kara aure please zan mishi biyayya." Murmushi tayi sannan ta ce mata. "Ni na tambaye ki ne? Ko nace ki gaya min wani abu?" Banko kofar dakin aka yi. Tana huci ta nufi Sarah zata rufe ta da duka. Ummi ta rike hannunta, "Ji mana a gidana, Sashina, wurina, zaki so ki tab'a wani! Ba zaku hukunta ta ba sai bayan bata idan ya so sai ki kashe ta yadda yayi miki." Fauce hannun ta tayi, tana me fisgar ta. "Sultanah Badi'atul Noor, ki albarkaci rayuwata da auren Prince Aliyu Queen Mother ki saka idanu akan bayin ki, ki saka idanu akan su wallahi ana son a tur...." Daga stairs Hajiya Suhailah ta tunkud'o ta, juyawa tayi suka hada idanu da Sultanah ta d'aga mata kafad'a. "Idan kin so ko kashe ta i don care, abin da nake bukata na samu tow me ya rage? Wannan rayuwar ta ce da ke kanki." Nad'e hannu tayi a kirjin ta. "Kin zata zaki cigaba da gudu ne? Bari ki ji ina shiri ne kafin ta kife, sai na jijjiga duniyar ki Badi'atul Noor" murmushi Ummi tayi sannan ta ce mata. "bayan nasan duk gudu na dole zan waiwaya ai, kuma zan dawo kanku ki fara gudu Suhailah kafin na gane wacece a tsaye a gabana." Zata bude baki, "wuce kafin na kira Jami'an tsaro su tafi dake sai a matse ki, ki fadi abin da yake bakin ki fadi abin da baki shirya ba. Tabbas ina gudu sosai nake gudu yadda ba zaki iya tadda ni ba. " Haka ta dauki yarta suka bar part. " Wallahi kika tona min asiri sai na kashe ki, sai na tabbatar baki raye." "Me ya rage? Me ya rage min, ina son shi kin sa ayi mishi asiri domin ya haukace a kaina, yau na haiuka ce." Buge mata baki tayi. Ta ce. "Wata zai aura wanda ya gaya min ba zai min kaarya ba." Flash back. Ranar da Ummi take waya da Abuturab akan Case din Sa'ade, a gaban uban dawaki take maganar hankalin ta akwance ta gama maganar, sannan ya kira Rumaisah ta gaya mata cewa yarinyar da Abuturab yake so, zata dawo daga london hutu. Don haka zasu je sokoto ganawa da iyayen Yarinyar. Tayi haka ne domin sanin alaƙar su da Ubandawaki kuma abin dad'i ta daki lambar daidai inda take bukata, dake Gulma yana cin sa, bai fadi abin da ya kawo shi ba, haka ya tattara ya je ya gaya mata, tun da ya gaya mata Sarah ta haukace, kamar zata mutu. Abin tausayi haka Uwarta ta hanata tafiya. *** Sokoto. Wato Abdul ya zama kamar bindi wa Malam Aminu, hidima sosai yake mishi yana tula mishi kudi, tare da mishi hudubar banza. Yau ma wasu manyan shadoddi ya shigo mishi da su. Dake a kofar gida suke haduwa baya yarda Yaransa su san Abdul yaba zuwa, idan aka zauna a can asibiti ana zagin Abdul da Uwarsa, cewa yake" hakuri ya haifa Arziki idan aka yi hakuri matar mutum kabarin sa, ai ko babu kome kar dai a manta ni ne Uban sa'adatu ahto waye baya kuskure " idan ya fara fadar haka shiru ake a ki kula shi, domin kuwa ana yin gaba kaɗan zai fara kawo musu alkhairin Abdul da yake mishi. Idan haushi ya ishi Inna Laminde sai ta fashe da kuka ta na faɗin. "in sha Allah Sa'adatu ba zata koma wurin wannan yaron da uwar shi ba, gara na mutu da naga komawarta hannun sa." Tana fadar haka baki daya yake dauke wuta. Dalilin haka jininta yake hawa, domin baki daya al'amarin yana bata tsoro, shi yasa ta ce Abuturab ya kawo sa'ade ta ganta. Ya koma da ita, kawai bata son ganin yarinyar a kusa da ita, kar ya sayar da ita yadda take ganin take-taken shi. Shi yasa yaran suka hana shi asibitin, yanzu haka yana zaune a kofar gidan Zakaria. Idan ya bushi isa yakan ya tafi bakin hanya ya sayo kwai da kwai, burodi, kosai da kosan rogo. Idan ya sayo sai ya shiga dakin shi na baki da yake kofar gidan. Sai ya cinye sannan ya fito da yar karamar Radio din shi, ya kunna yana shan labaran duniya. Yana zaune ta hango Abdul yayi ya washe baki, parking yayi ya fito da manyan laidoji. Har kasa ya gaishe shi. "Baba gashi wannan namar kilishi ne" ware manyan idanun shi yayi ya ce. "wato yaron nan kana son ka sa ni naji maraya ta fi karkara, kaga yadda ba hada yan kumatai. Allah yamaka albarka." Amin ya bude ya fara ci. Sai da ya bari ya nutsu acin namar Abdul ya ce mishi. "Baffa anya kai ne ka haifi sa'ade?" Murmushi yayi bayan ya cika bakin shi da namar kilishi. Ya ce , "Duk Yarana kuwa babu kyakyawar ta, domin nima nasan na haifi kadara me tsada, yo don dai kar a saka ni a bakin duniya ne ai sai nace Sa'ade ai sai shugaban kasa wanda zai na biya min kudin zuwa dakin Allah da kai ziyara kabarin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, duk shekara ina bisa jirgi ina kashe kwarkwatan idanu idan na dawo na bawa Malam Kalla labarin ganin dakin ka'aba." Murmushi Abdul yayi ya gyara zama ya ce mishi. " Baba idan ka shirya sai na kai ka umra nan da sati daya ka tafi kafin wancan matsiyacin ya dawo min da ita, amma Baba maganar gaskiya idan yadda kake saka min albarka haka zaka tsaya min na samu sa'ade da na more. Kai ne uban Sa'ade bai dace ace kana tsoron wani ba." Wato Abdul yayi ta iza Malam Aminu akan dokin bera, kallon shi yayi sai da ya gama ya ce Mishi. "Abdulhakimu, ka tab'a takun saka da Abuturabu kuwa?" "Mun yi akan Sa'ade a can ƙasar waje." "Baka yi ba, idan da kayi zaka gane abin da nake son gaya maka, shi din wani irin mutum ne da matukar ya ce abu na shi ne, tow ba makawa nashi ne. Baka yi mamaki yadda aka yi har yaji labarin abin da ya faru? Tow wannan shi ne ake kira karfin iko, Abdul shawara daya zan baka kuma zan maka iya iyawata shi ne idan ya dawo da ita, kasan yadda zaka goge laifin ka a wurin Sa'ade, matukar ta yafe maka ni kuma zan yi amfani da yafiyar na saka a baka matar ka" shiru yayi sannan ya ce mishi. "kana gani zata amince ta dawo wurina?" "Kai ba namiji ba ne? Me yasa da ta ga Abuturabu ta bishi?" Shiru suka yi kafin ya ce. "Idan har kasan yadda mace take tow, babu amfanin ka saka kanka a damuwa, Abuturabu ya san motsinta da abin da take so ne, Abuturabu yasan adadin damuwarta da abin da zai saka kuka kayi kokarin gano haka, shi ne kawai zai baka Sa'ade matukar ka iya kyautatta mata tow zata iya manta abubuwan da ya faru ta dawo gare ka" shiru suka yi kafin Abdul ya kuma cigaba da zuga Baffan Sa'ade, shi kuma yana gaya mishi yasan hanyar da zai shawo kan Sa'ade, da wannan Haukar Abdul ya bar gidan yana cin alwashin sai ya karbu abarsa. *** UK... Hospital... ( Gaskiya wannan labarin da tsawo yake 😏😠Allah ya gani naso na gama kafin sallah layya😌😣😢 amma abin ya ci tura ko na datse wani wurin ne?)🤣😃😆 [23/06, 9:53 am] usmanlauratu71: 47..........*BARKA DA JUMA'A* Cikin matukar nasara aka yi dacen binciken kunnenta, an gano ya jijjiyar ta kumbura ce, don haka suka bashi shawaran aiki za a mata amma sai sun daurata akan magani na tsawon watanni kamar uku zuwa hudu. Kafin ayi aikin domin bai yiwu a mata aiki a yanzu ba, dole ana son tasha magani wanda ana aikin kome zai koma daidai, maganar ce dai sai a hankali. Domin sun yi tabbatar zata yi magana amma shima gaskiya zai iya daukar wasu shekaru ko watanni idan aka yi sa'ar mata aikin. Godiya yayiwa likitan sannan ya ce mishi. "Kenan sai an fara yin aikin kunnen kafin ayi na bakin?" "Eh Mr turab, aikin kunnen shi ne mai muhimmanci, na bakin babu wani muhimmanci domin bai zama dole ta yi magana ba, kuma akwai risking a cikin aikin bakin sai idan ka amince za a iya yi" wani irin Bala'in tausayi ta bashi, domin ko jiya sai da ta ce mishi. Tana son tayi magana da Innarta, ya dauki waya zai kira Nazifi ta girgiza kai ta ce ita tana son magana ne baki da baki, ita ba zata tab'a jin muryanta ba kenan haka zata girma har ta mutu ba zata ji voice dinta ba. "Dr babu wani hanya ce?" Ya tambaya a matuƙar bukace, shiru likitan yayi hana kallon Sa'ade. "Akwai hanya ɗaya kanwarka ce?" Shiru yayi kafin ya ce. "Yes kanwata ce" kallon su yayi sai kuma ya share ya cigaba da bincike a kan computer din sa kafin ya d'ago kai yayi sannan ya ce. "Akwai doctor Jalaluddin Quraish a Egypt mazaunin alkhirah shi zai duba bakinta, shi a fannin ya kware" rike hannun likitan yayi. "Na gode doctor ka gama min kome" murmushi likitan yayi, sannan ya rubuta musu magani. Ganin yadda yake farinciki yasata itama murmushi duk da bata san akan meye ba, ki akan matsalarta ce! Jan hannun rigar shi tayi ta d'age mishi gira daya. "Babu kome" ya fada yana jin kamar ya rungume ta. Amma aure ya musu iyaka. Haka ya sayo maganin a hanyar dawowa daga wurin sayan maganin ya hadu da Latifah. "Prince kun fito?" "Hmm!" Matsawa tayi gabanta, ya gyara mata zaman mayafinta yana me cire madubin ta ya sa mata a idanunta. Ya ja kumatunta, dariya suka bawa Sa'ade. Sai nuna su take tana musu alamar sun yi kyau! Janyota cikin su Latifah tayi, tana faɗin. "Prince kayi flight for her, ka karbo ta she need you and you need her, you guys need each other, damar ka ce ka amso damar ka ce ka hakura da ita, but kun matukar da cewa da juna" daga haka ta juya abin ta. Murmushi yayi ya ce. "Tow na gode likitan Prince." Ya juya yana me barin asibitin shi da Sa'ade, itama juyawa tayi tana kallon shi, tabbas samun namiji irin sa sai an shirya. Tow na gode likitan Prince! What? Ya karɓe ta kenan a matsayin matar sa? Kai ina impossible! Shi kan gwani daga asibitin park ya tafi da Sa'ade, wayar shi ce tayi kara. Ya ɗauka tare da sakawa a kunne ganin lambar london din ce." Assalamu alaikum!" "Mutuwar ka ce ta kira ka" murmushi yayi sannan ya ce. "Mutuwa ta, na san ba zata kira ni ta waya ba. Sai dai lusari ai na jima da zuba idanuna ija jiranka sai yanzu?" "Kai Yaro baka san me yasa na barka a raye ba? Ko kana son na fara nuna maka wani abin burgewa ne?" "Me ka isa me? Allah ya raya ni bai kashe ni domin wa'adina da saura kai din banza ne zaka ce ka bar ni a raye?" Yaja tsaki. "Hahh! Ina yarinyar da ka tawo da ita?" Idanun shi ne ya shiga niman Sa'ade, can ya hangota tana gudun zata tawo wurinsa wasu yan iska suna binta. "Ka d'aga kafarka sai na harbeta domin an saka bindiga akan ta " kura mata idanu yayi ya hango tana gudu, wani jan abu yana bibiyarta. "Ka yarda na Barka a raye ne?" Bai tsaya sauraron kiran ba, ya nufe ta da mugun gudu, ganin irin gudun da suke yasa security din park din bin wadancan mutanen, shi kuma ya bude mata hannu ta shige jikinsa. Harbin da aka sake ɗaukar a wuce ta saman kanta, suka fadi can, rufe ta yayi yana kallon fuskar ta. "ya isa haka" ya fada mata. Hawaye ne ya zubo mata. Security din ne suka zo wurin su. "Da fatan baku ji ciwo ba" "eh ya d'ago ta. Sai lokacin ya lura da wayar shi da kayan maganin ta. Dauka yayi ya saka a kunnen shi. "kai banza idan nayi maka laifi ka tsaya a kaina, matukar ka tab'a yarinyar nan sai na kashe ka mugun kisar da a tarihi babu irin sa." Ya kashe wayar yana jin kamar ya fasa ihu. Riko hannun Sa'ade yayi ya nufi wurin da ya ajiye motar sa ya bude ya sa, sannan ya zaka zai shiga wayar shi ta kuma ƙara. Cizon lips dinsa tayi kamar ya fasa ihu. "Waye kai ne?" " Da farko baka razana ba, me yasa ka razana yanzu? Anya ba cin amanar matar ka kake ba? Hhhh ko da yake babu ruwana a cikin al'amarin but me zai faru idan na tura sakon hoton dirty affairs da ake tsakanin ku" kashe wayar Abuturab yayi ya taka motar suka bar wurin. "Koma waye sai na kama shi" ko da suka isa gidan, abinci ta ci ya bata magani ta sha. dake dare da yayi ƙwanciyar tayi a falon domin tsoron da ta ji. Shima a wurin ya kwana yana gadinta har asuba, ya tashi ta zuwa daki ya wuce masallaci. Da misalin ƙarfe biyar na yamma Ra'is ya iso, sake ya dauki hutu a wurin aikin sa, shige da fice suka yi ta yi har washi gari abu daya suke, ranar Alhamis da yamma suka baro gida har da Latifah zuwa airport. Rungume juna suka yi. "Ki ajiye min abu me dadi kafin na dawo" hawaye ne ya cika Idanunta. "Prince ya amshe ni ne?" "Fiye da haka, Prince ya amshi likitar sa" "Prince Lucky fa?" "Kina bukatar ta ne?" "Eh nayi magana da wani makarantar kurme a Liverpool sun ce a kaita" kara matseta yayi ya ce mata. "thank you, amma sai abin da hali yayi." "Ka sato mana ita ka kawo kafin musha bikin future queen " Jan hancinta yayi bayan ya sake ta. "You are my queen" sarkafe hannun juna suka yi, Sa'ade na kallon su. Sai dai yau amadadin su burge ta haushi suka bata, don haka ta dauke kai kamar bata gane abin da suke yi ba. A gefen ta Ra'is yana ta janta da hira, duk da hankalin tana yana kanshi, amma baki daya nutsuwar ta yana kan su Abuturab. A lokacin da suka gama sallama jirgin su zai tashi. Suka mike baki dayan su, har da ita zuwa Latifah tayi ta rungume ta, tana bubuga bayanta. Haka suka rabu domin ita kan Sa'ade tace a ranta ba zata dawo ba, kawai zata zauna a wurin Innarta. Koda suka shiga jirgin dauke kai Sa'ade tayi tana hararan shi, sai cika take tana batsewa, kamar ta rufe shi da duka, sai wani rungumar Latifah yake haushi yake bata. Shima a bangaren shi, bai san ya mata laifi ba amma ya lura da fushi take da shi. K Sun sauka a lagos, inda suka huta sannan suka biyo jirgin Sokoto, ranar Juma'a. Kafin a shiga salla juma'a suka sauka a kan wuri, tunda suka iso Sokoto take masifar daukin ganin Innarta. Sai bayan sallah juma'a, suka wuce gidan Zakaria. Malam Aminu yana kofar yana cin kilishin sa. Tana son fitowa amma tsoron shi yasa ta kifa kanta a cinyoyinta. Fitowa Abu turab yayi ya nufi inda Malam Aminu yaƙe, ya tsaya hannun shi a cikin aljuhun wandon shi. "Yalli jam!" Da sauri ya d'ago kai suka ido hudu, bai san lokacin da ya taune harshen sa ba. "Innalillahi!" Ya fada tare da ware idanun shi. "Aliyu" "Na'am ya muka yi da kai?" "Bayan ka biya kudin da na sayar maka da ita ka kuma bani dubu dari da hamsin kudin sadakin ka da yarjejeniyar saka hannuna, shaidun sun hada da Mai gari, Malam Musa kalla sai Innar su." Sosa kunnen shi yayi ya ce. "Me yasa ka ci amana ta?" "Wallahi asiri aka min!" "Meye hukuncin ka?" "A kai ni asibitin mahaukata domin na haukace " tab'e baki yayi ya ce mishi. "Nasan Abdul yazo ba sau daya ba ba sau biyu ba, don haka duk kudin da ka ci a wurina na baka kyauta!" "Allah da gaske?" "Zan kara maka wani ma sai dai ka sani ban yarda sa'ade ta fito ko da kofar gidan nan ne yayi maka? Sannan zan baka gida me kyau anan garin, sai ka gaya min abin da kake so." "Innalillahi ni ne da gida a birni? Tow kace na fadi abin da nake so? Wai dakin Allah zaka.kai Ni" "tashi Baffa." Ya fada mishi ya taso. "Ka sani idan ka kuma cin amanata sai ba saka sojoji sun tafi da kai kasar waje inda ake tadda nakiya da harbe-harbe." "Yanzu d'an nan meye yayi zafi?" "Babu kome Sa'ade kawai nake so a kula min da ita " "dan nan ko kaina kace na cire na bata ai dole na bata " "yawwa zan maka abin da baka zata ba" "da fatan ba kai ni can zaka yi ba" juyawa yayi ya fito da Sa'ade ya nufi wurin shi ya damka mishi ita. "gata nan" sannan ya koma boot ya dauko kayanta da wata karamar jaka, yana zuwa ya mikawa Malam Aminu, ya nufi hanyar cikin gidan ita kan tsoro ya hanata motsi juyawa yayi ya sakar mata murmushi. Jikin Baffan ta kuwa rawa yake domin ya gagara hakuri sai da ya bude jakar. Rufe baki yayi ya ce. "Aliyu? Wannan kudin na me ka bani " "miliyan biyu ce, na baka domin nasan kana son kudi zaka sayi shanu " "Ai na gayawa Abdulhakimu, kai kafi da cewa da Sa'ade kun ga kyauta ba irin tashi ba na atsakura maka ba, ah tow wallahi ka ce min ka siye ta na yarda ma." Da sallama Abuturab ya shiga cikin gidan, suka zaune a tsakar gida, sun gama draman su kenan da baffa, sai ga Abuturab da Sa'ade. Makalewa tayi a bayan shi. Tana leka Innarta. Mika mata hannu tayi da sassarfa ta isa jikin Inna, ta fashe da kuka. Irin kukan shagwab'a nan wato sakalci gaban uwa. Shafa bayan ta take tana kallon Abuturab. "Bansan yaushe Iyayenka suka haife ka ba, sai dai nayi imani Matar da ta haife ka Jarumar mace ce a duk cikin al'amarin ta, ta kuma haifi shugaba a cikin al'umma masanin adalci da dattako. Ka godewa Allah lahiranka tafi duniyar ka kyau." A ranshi ya ce. *idan duk wannan Addu'oin domin abin da nayi ne, tabbas zinariyar gabanki nake bukata a matsayin tukwaici* a kan fuskar shi murmushi ne a kwance. "Amin Ya Allah " ya fada a sanyayye. Matsa mishi tayi ta ce. "Zauna Aliyu haidar" zama yayi yana murmusawa. Aikuwa Sa'ade ta wani narke kamar an sawa sugar ruwa. Tana zuba iyayi nan ita shagwab'a. Sai murmushi Inna Laminde take. "Laminde kin ga haihuwar Arziki yanzu yaron nan ya kawo min miliyan biyu, ko Aliyu? Ina ce ban roke ka ba, kuma kace zaka biya min hajji..... (Idan kece Inna ya zaki yi da Man Aminu?) 08130269641 ban sani ba ko zan samu lokaci nayi Barka da juma'a, idan ban samu ba kuyi maneji in sha Allah gobe sai mu daura [23/06, 8:38 pm] usmanlauratu71: SALLAH PROMO 💫🌟SALLAH PROMO ✨💫 SALLAH PROMO 💫⭐️ Kuna ina matan kwalisa ga GHT product ciniki,ciniki kyauta, kyauta💃💃🤩 Royal jelly 5500💃💃Instead of 6500 Ganoderma 5500💃💃instead of 6500 Garlic oil 7k💃💃instead of 8k Myco balance 7k💃💃instead of 8k Female care 12k instead 13k B clear 13kninstead of 14k Hijabis Ana bada half kuma Inka siya kayan d sukakai 20k zaa mama free delivery to wane state ne in shaa Allah 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 Hanzarta Ki mallaki naki kar ayi gyaran sallah ba ke😁😄 Domin mallakan naki Ki tuntubi Wannan numb👉 07063579004 48....... "Kai da wallahi baka da hali, yanzu karban kudinsa kayi bayan duk abin da yake faruwa? Anya Malam kasan Annabi yana Madina kuwa?" "Na sani ma idan ba so kike ki kafirta musulunci na ba" takaici ya saka ta dauke kai. "Aliyu ka ga irin abin da take min ko?" Murmushi yayi ya ce masa."Innata bata da matsala Baffa kai ne matsalar Innar mu" shiru yayi sannan ya cigaba da cewa. "Tana bakin kokarinta kana kara ruguza mata farin cikinta, babu uwar da zata yarda a sayar mata da rayuwar yar yarinyar ta karama, kasan yadda uwa take fafutukar ta rayu domin Ya'yanta kuwa? Ko kasan yadda Uba yake sadaukar da rayuwar shi domin ta yaran shi tayi kyau, Baffa idan kana son wani abu ka kira ni waya zan baka zan maka amma rayuwar Sa'addah wani abu ne mai muhimmanci,idan ka barta ta yi farinciki ba zata manta da ita ba, lokacin da aka raba ni da mahaifiyar mu naji zafi amma ita ta tsaya min tare d wanke ni daga zargin da ake min, Yayuna biyu sun rasu sakamakon wani abu na daban, mahaifiyar mu ita ce take tsaye a kanmu. Mahaifiyar mu da namiji ce babu abin da ba zata yi domin Ƴaran ta ba. Amma wani ikon Allah sai ta zama mace me kamar maza, tana kallon kome a tsannake take hukuncin sa. idan na gaya maka daga gidan da na fito ba zaka yarda ba, ni kuma ina son koda wata rana ka san daga zauren da na fito, Innata ina kyautatta zaton wani sati zamu shiga kotu. Domin ina son na koma kan da wata uku. Amma komawar tawa da Sa'adda ce, domin a mata aikin kunne da baki. Inna nazo na gaya miki ne za a mata aikin kunnen ta daya, idan kin amince zata tafi har da karatu. Amma alfarma ce nake nima. Idan ta koma gidan mijinta shi kenan" "ko bayan raina Aliyu ban yarda Sa'ade ta koma gidan Yaron can ba, marina uwarsa tayi, me yafi haka muni? Ban cire maka kome akan Sa'ade ba, kayi duk yadda ya dace da ita, amma na haramta mata zama da Abdul ko da kuwa ana mutuwa a dawo, ban amince ba idan kuma ta ce shi take so na rantse da wanda rayuwata da Mutuwata take hannunsa na yafe ta duniya da lahira." Dake daya kunnen da take ji ta juya da sauri ta mike tare da fashewa da kuka, tana girgiza kai. "Inna bata da laifi fa" "na sani sai dai bani da wata hanyar da zan iya gaya mata abin da zan aikata ne dole sai ta haka" ajiyar zuciya ya sauke. Malam Aminu yana rungume da jakar kudinsa. Kiransa Ra'is yayi yana faɗin. "dan iska ka manta da ni ne?" "Ok gani nan fitowa, tow innata zan tafi" Sa'ade tana kwance jikin Innarta ta d'ago kai tana kallon shi. "Ina zaka?" Ta tambaye shi tana tura baki, "Mijinki zai zo anjima kar ya fasa min kai". Rau-rau tayi da Idanunta zata fara sana'a. "Sai an jima Innata" "Yawwa kun gama Yaren kudar ne?" "Laaa Inna kema kin san muna Yaren kuda ce?" "Hmm Abuturabu kenan Allah ya bamu lafiya" "Amin Ya Allah" ya fada yana musu sallama, har bakin kofar gida Inna ta rako shi, Allah sarki Malam Aminu rike kudin sa yayi gam yana tsaron kar a kwace mishi, "Inna gashi ban zo muku da kome ba" "Ka kawo min Sa'ade shi ne komen da ka kawo min haka ma ya ishe ni" "Na gode sai na zo" "Allah ya amince." Ta juya ta koma cikin gidan. Bayan tafiyar Abuturab kuwa sai ga Abdul, tunda yayi sallama a kofar gidan Baffan Sa'adatu ya leka suka yi idanu ya ce mishi. "Baffan Sa'ade, naji labarin kunyi baki kamar Abuturab ne yazo da Sa'adatu?" Hàdiye yawun bakinsa yayi ya ce mishi. "Eh tow kuwa kayi gaskiya yaro, shi ne amma kuma bai zo da ita ba." Yasan halin baffan don haka ya ce mishi. "Baffa ba dai kayi amai ka lashe ba? Sa'adatu mata ta ce tow akan me za a hana ni mata ta? Baffa kasan ba zan yarda ba." "Kasan dai Babarka ba yarda xata yi da maganar auren ku ba, sannan ita kanta Babar Sa'aden ba yarda zata yi ba, abin da za ayi shi ne ka fara lallaba Babarka sai ka zo nasan yadda zamu yi da Sa'ade, amma kafin nan an jima ka ciko ƙatuwar leda da kayan zaki, ka kawo sai na shiga da kai ka ganta kasan Uwaye mata basu da matsala idan suka ga kana bibiyar yaran su. Take zasu sauke su baka yaransu din." Yadda Malam Aminu yake tsara Abdul ya zata zai ci nasara ne sai ce mishi yayi. "Matukar na gano ha'intatta kayi sai na yanke wuyarka, na kuma sace Yarka na rantse." "Akan me zan ha'ince ka? Ai tuntuni na gaya maka gaskiya ka ce na yi kokari na a matsayina na uban Sa'ade ko ba haka ba? Yanzu kuma uwar me zan maka? Ko dai abin da Babarka ta min zaka min?" Yadda yayi maganar yana tsare Abdul Hakim da idanu, sai ya baka dariya har wani tsumewa yayi irin bana son maganar banza. "Shi kenan Baffan Sa'ade, sai dai wallahi na fahimci ana min zagon kasasai na baka mamaki." Ya juya ya fice wani karamin ajiyar zuciya ya sauke, yana shatce gumin da yake karyo masa. Lallai kowa yaci buzu dole yayi aman gashi. Wasa wasa Abdul da Abuturab suka mannawa Malam Aminu hauka tuburan , abin dariya idan Abuturab yazo da safe to da rana Abdul zai zo, kuma sai Allah ya saɓa ganawar su. Har aka samu sati biyu nan ne Abdul ya fusata domin ya fahimci wasa da hankalin shi Abuturab yake shi yasa ya haɗa mishi rashin arzikin da Malam Aminu. Yau da ya kama Monday ya shigar da karar Malam Aminu da Abuturab, shi kan sun tafi Maikulki da Ra'is, domin ya sayi babban fili har an zagaye mishi filin za a fara aikin gida babba da lambun zamani. Shi yasa bai san meke faruwa a cikin gari ba, a gefe guda da gayya yake ta zubawa Malam Aminu kudi yana kuma bashi shawaran duk wanda ya bashi aikin kudi ya ci ai ba kiran shi yayi ba, shi yasa da Abdul ya gaji da renin hankali ya maka su kotu, na farko shi ne sun kwace mishi mata Abuturab ya tafi da ita, sannan Malam Aminu yana cin kudin sa haka kawai ba tare da ya bashi matar sa ba, bayan da auren su. Wannan sune korafin Zakaria ya kira Abuturab ya gaya mishi. Dama abin da yake jira kenan shi yasa ko kwara bai tafi ba, ya tsaya ayi uwar da za ayi ya shirya Hajiya Daulah tsaf. Tare da taimakon Yarima Sadeeq da wasu abokan sa uku suka tsayawa Abuturab, sannan ga Ra'is na huɗu abin dai ya firgita Abdul amma dake yana son matar sa Uwarsa ta kawo sabon idea, wanda take fatan yayi. Shi yasa basu wani dauki lauyoyi ba, daya kawai ya ishe su. Ranar Juma'a za a fara zaman sauraron kar'ar....... Allah ya ba me rabo sa'a [25/06, 10:11 am] usmanlauratu71: 49.....(In order to really love someone, you must love him as though he was going to die tomorrow. - arabian proverb) Sauraran kar'ar su, sai karfe sha biyu da rabi na rana, karfe sha daya ya musu a cikin kotun, tun a kofar shiga kotun Abuturab suka hadu da Abdul, komawa bayan Abuturab Sa'ade tayi. Cikin bala'in tsoronsa, murmushi Abdul yayi ya ce musu. "Da alamu dai kazo da kwarin gwiwa zaka koma da sanyin gwiwa" smirked Abuturab yayi mishi yana sanye da sunglass na Pume, ya shiga cikin kotun. "Me yasa ka share shi ba kai magna ba?" Kamar ba zai magana ba, sai ya ce. "Idan na kula shi na zama kare kenan da duk abin da aka min zan ji haushi har nayi barke. Haka suka shiga cikin kotun Inna kan taki zuwa ta ce, zata zauna a gida tayi ta musu addu'a. Don haka sai da aka sauarri kara daya kafin nasu. Iya lauyoyin Abuturab kawai suka tsaya da Sadeeq wanda ya zo ana tsaka da shari'ar. Sai dai kuma lauyar Abdul ya musu wani irin tufka da abu turab ya kasa kunce kansa, na farko an zarge shi da ɗaukar matar aure ya tafi da ita wata ƙasa, wanda suka kawo ayoyo daga suratul Nisa'i, sannan ya kafa hujja da suratul Noor, bayan hadisai da litattafan Bukhari da Muslim, sannan ta tafi babin muharrami ya kafa hujja da shi a cikin littafin fiqhu. Sannan aka zargi Sa'ade da laifin bin mijin da ba nata ba, tare da hukuntatta da laifin aikata mugun barna. Shi kuma Abuturab an tura shi gidan gyara hali sai ranar bakwai ga watan march. Ita bulala za a mata. Hankalin Abdul ne ya tashi ya rasa yadda zai yi domin baya jin yana gani za a zane Sa'an shi ba. Magana yayi da lauyan su. Shi ne ya samu magatakarda ya mishi magana shi kuma ya samu alkali da maganar kar a zane Sa'a. Kus-kus suka yi sannan magatakarda ya koma wurin zaman shi. "Bayan sauraron bayani daga bakin kowani bangare kotu zata tura Aliyu gidan gyara hali, ita kuma Sa'ade kotu zata mai dawa Abdul matar sa." Wani irin dafe goshi Abuturab yayi yana kamar ya fasa ihu. Shiru kotun tayi. Haka suka fito jikin kowa a mace, kuka Sa'ade take domin kota bakinta ba abari an ji ba. A bakin kofar kotun Abdul ya fashe da dariya. "Yaro man kaza, na gaya maka Sa'ade tawa ce, sai dai a kare a gidan dan Kande, jikan masu haihuwar sheggu." Murmushi yake Abuturabu ya mishi, ya ce mishi. Sayan alkalin ne ya saka ka farinciki ko tursasawan ka? Tausayi ka bani amma bari zan nuna maka yadda ake abin saka idanu kaga ga Lucky Allah ya baka sa'a." Wucewa da Abuturab ganduroba suka yi. Ransa ya b'aci amma yasan ba zai tab'a wuce awa biyu a wurin ba. Akan idanun shi Abdul ya tafi da Sa'ade sai kuka take. Bakiɗaya sai ya tsinci kansa da wani irin kunci. Sadeeq ya kira Sultan of Sokoto, wato mahaifinsa ya gaya mishi abin da yake faruwa. Dake abu ne na manyan kuma governor din sokoto, kusan D'a yake a cikin masarautar sokoto. Haka yasa kai tsaye aka bada umarnin a sake Abuturab. Babu shiri Ganduroba suka tsaya su Sadeeq suka dauke shi. "Kuyi hakuri" "ba kome" ya fada yana karkad'e rigar shi, ba alfahari ba shi dai yasan ba zai tab'a zaman gidan yari ba, domin bai yi kuskure ba. Kuma wallahi sai ya kure Abdul Hakim da uwarsa. Daga nan kan wuri suka koma. Kasa zama yayi baki daya hankalin shi a tashe yadda yake, hango kukan Sa'ade ji yake kamar idan ya kama Abdul ya kashe shi har lahira. Amma haka yayi ta rarrashin zuciyar shi, har sai safa da marwa yake. Idan ya tuna tana hannun Abdul, ko wurin Inna bai kome ba, "Prince ka kwantar da hankalin ka mana" "like how? Gaya zan kwantar da hankalina bayan hankalin baya tare da ni, ka ga ne abin da nake nufi ko na kara maka bayani, yarinyar ita ce hankalina da nutsuwata, infact ko ban same na ba, sai na tabbatar ta samu adalci. " Ya zauna yana dafe kansa. Shiru suka yi sannan Sadeeq ya ce."akwai alkalin da zamu tuntube shi ba sai anyi zaman kotu ba " "kana ganin yaushe kenan?" "Ka bari wani sati sai na gayawa Maimartaba, ko zuwa gobe za ayi ta ta ƙare." "Why not mu gaya mishi before sallah Juma'a" riko hannun shi Sadeeq yayi ya ce mishi. Ka nutsu mana!" "Kaga ba gane mishi zaka yi ba, domin ya hau bishiyar kace" juyawa Sadeeq yayi yana kallon Ra'is ya gyada mishi kai. "wallahi ya haukace a so kawai ka bar shi mu bishi da addu'a idan ba haka ba, kuka zai mana." Wuka ya dauka zai bi Ra'is. "Dan iska na kyale ka zaka min Iskanci ko ba so ba, idan yayi rape din yarinyar fa, baka da tausayi ne?" "Ina da shi mana, karshe ta zama bazawara shi ne gaskiyar maganar." "Yo ai dama bazawarar ce." "Me sauki ne ka ga ni ka bani aurenta kawai." Shiru Sadeeq yayi yana kallon su. Kafin ya ce musu. "Aliyu taya me yasa kace zai rape ɗinta?" Tsaki yayi ya ce. "Baka ganin kome ba ne? Kome da karfi yake." "Amma dai ai bazawara ce " "eh duk da haka ina tare da ita,ko da mazan duniya sun maida ita kamar kofar wucewar su ce. Ina tare da ita." Shiru suka yi kafin Ra'is ya ce mishi. "wani irin so kake mata" "yanzu dai mu nufi wurin Maimartaba nasan zai ta zuba idanun ganin mu." "Baka ba ni amsata ba" "soyayya zai iya karewa kauna kauna yana nan abadanda'iman" haka yasa suka yi shiru, tare da nufar cikin gidan. "Umma ina Abba?" Sadeeq ya tambayi Mahaifiyar su. "Yana masalaci bai jima da tafiya ba" "ok Umma" ya fita wurin su Abuturab. Masalaci suka wuce amma zuciyar su babu dad'i. Haka suka nufi masallaci. Sai da aka yi sallah asar suka samu ganin Maimartaba, Abuturab ya gaya mishi kome, shiru yayi sannan ya saka aka kira liman babban masallacin fada. Aka kira shi dake babban alkali ne me matsayin Gran khadi, kuma aboki ne ga Sultan. Anan suka tattauna aka shiga niman Dr Sharif. Sultan da kansa ya kira shi, ya ce yana son ganin sa maza da yar da dansa yake aure, sannan a kira mishi Malam Aminu da Inna. Yana son ganin kowa har da Hajiya Daulah baya sallah isha. --- Tunda suka bar harabar kotun take kuka, ba karamin haushi abin ya bashi ba, ya zuba mata ido kafin ya ja tsaki ya cigaba da tuki. Yana isa gidan shi aka bude kofar, ya shiga bai jira me zata yi ba ya fito ya bude kofar inda take zaune ya shiga janta cikin gidan, a falo ya watsar da ita kamar ya samu kayan wanki. "Meye Abuturab ya fini da shi " ya fada da ƙarfi, dake ya fada ta gefen kunnen da bata ji bata san yana yi ba, cire kayansa yayi ya nufe ta, ta fara ja da baya wani mugun tsoro ya fara kamata, kar abin da ya faru ya sake faruwa. Kuka take tana rokon shi amma fir ya ki kyale ta, sai da ya wulakanta kayan jikin ta, da nufin ya biya bukatar shi ko da karfin tsiya ne, sai dai yana isa wurin. Ya samu tayi bako me jan mota. Takaici ne kishi ne, haushi ne, bakin ciki ne yasa shi rufe ta da duka, sannan ya bar ta babu kaya, tun karyawan safe babu kome a cikin ta. Haka ya fita ya bar ta a wulakance, bai dawo gidan ba sai karfe shida na yamma, tana kwance ya wurgo mata abaya ta saka, ganin ya nufo ta yasa ta ja da baya, kirjinta ne suka dauki hankalin shi, yasa shi zuwa sai da ya gama jagwalgwalata, haka kawai yake jin kiran da Babansa yayi mishi babu alkhairi, don haka ko ganin kazanta da take ciki bai yi ba, ya matseta ya shiga tura mata macijin wandon shi, zaro idanu tayi domin wannan shi ne first time ɗinta da haka yake shirin faruwa, cizo ta yanka mishi me karfin gaske wanda ya rike fatar kafad'ar shi. Da sauri ya buga haɗa ta da bango Ya tashi domin baki daya ya kasa shiga saboda tsantsin jini ya hana shi shiga. Yana tashi ya lura da tunda ya buga kanta da bango bata kara motsi ba, tsoro ne ya kama shi, domin har fuskar ta akwai shatin yatsunta ban da jikinta da ya zane ta kamar yar shi, duk bakin cikin shi me yasa tafi son Abuturab da shi. Haka ya saka mata kaya, domin dole ya je da ita. Tunda mahaifinsa ya gaya masa su hadu a fada kan wuri. Ruwan sanyi ya dauko a firij ya watsa mata, ta ja a ajiyar zuciya. Abayar ya mai da mata, sannan ya kwashe ta haka suka nufi fada, a unguwar yayi Sallah dake bata da karfin tashi ya bar ta a mota. Sai bayan isha suka shiga cikin gidan. A babban falon Maimartaba suka samu kowa da kowa. Fuskarta a kumbura ainun, sam abu turab ya manta inda yake ganin ta yasa shi mikewa, ya nufe ta ganin yadda ta kuma rikice mishi da kuka yasa shi kara kidima zai nufe ta Abdul ya sha gaban sa."iyalina ce" ture shi gefe yayi yana kallon fuskarta. "Waye ya dake ki? Waye ya mike haka?" Ya tambaye ta da hannu, Ture shi Abdul yayi yana daka mishi tsawa. "Ka kyale min iyalina mana!" "Ka ga bata kai nake ba, Me ye ya same ta?" "Baba karami!" "Na'am Abba" ya juya kamar sai yi kuka yana kallon Maimartaba. "dawo ka zauna." A rikice ya koma bakidaya autancin yana son motsawa ne, Bayan an bude taron da addu'a, sannan aka tambayi me ya faru. Abdul ya fara magana. "Allah ya baka nasara don mun samu matsala da mata ta, shi ne aka samu yar arashi na rashin fahimta har aka rufe mata ta a wurin hukuma, tow dake suma nayi shi yasa haka ya faru. Amma ina son matata wallahi" "Abuturab me ya faru?" Gyara zama yayi muryan shi a sanyayye ya ce. "Allah ya baka nasara, an nime aure a cikin aure, domin na riga da na biya sadaki da na gani ina so da sahalewan Sultan, ga yarjejeniyar Mai garin Maikulki Alhaji Hashim ya nima min auren ta, ga Mahaifin Sa'adatu nan." Shiru falon ya dauka. "kira min Mai garin Maikulki!" Ciro wayar Abuturab yayi ya kira. "yallabai Barka ya gidan!" Alhamdulillahi. Maimartaba yana son magana da kai ne" "Masha Allah, tow Allah yasa lafiya" tambayar shi aka yi ya bada amsa abin da Abuturab bai fada ba shi ya kara musu har da copy din takardan shaida aka basu, Inna ta fito da nata, Malam Aminu ya fito da na shi, Aliyu ya fito da na shi. Sallama aka yi da Mai gari aka cigaba da jin ba asin taya aka yi kome ya faru. "Malam Aminu me ya faru?" Nan ya shiga basu labarin abin da ya faru har da kai Sa'ade makaranta da kome da kome wanda shi bai yi kome ba, sai Abuturab. Shi a tunanin shi Abuturab ya tafi da ita ne, sai gashi a she bai tafi da ita ba, ganin wannan damar da shi ne ya bawa Abdul auren amma ya gaya mishi gaskiya Abdul ya ki ji, karshe kashedi ya mishi na cewa matukar bai bashi ita ba, wallahi tana komawa makaranta zai dauke ta, kuma suna da kudi babu abin da zai. "Ba wai na bashi don ina son abin duniya har haka ba ne, sai dai nayi imani da Allah da na lalata mata farin cikin ta, gara na hakura na bashi ita tunda yayi alkawarin zai lalata rayuwar idan ya lalata mata rayuwa ga nakasa da wanne zata ji? Shi yasa na yanke shawarar bashi auren ta, da ace lalacewa tayi gara a kira ta karamar bazawara " sake baki Inna tai tana kallon Malam Aminu ashe shima jarumi ne ta zata kaunar shi da kudi ba zai iya saka shi dogon nazari ba. Ya kara da cewa. "Ban amfane ta da kome ba, sai da bakin ciki tun girmanta, na zata haka da nayi zai saka ta samu farin ciki ne bayan shi da bakin ya ce ya dauke karatun ta. Sai gashi yana ta azabtar da ita, ko da aka ce ta kashe shi sai da nayi sati daya a kulle, wannan Yaron shi ya shiga ya fita aka sake ni tare da taimakon mijin Hajiyar nan da ta rufe ni, bayan ta mari Matata. Amma dake dan adam ne shi na gaya mishi ba zai iya karban Sa'ade a hannun shi ba, bai yarda ba Allah na tuba ko mutuwa nayi bana fatan Sa'ade ta zauna da Yaron nan, domin abin da uwar shi ta min har yau na kasa komawa garin Maikulki ta zubda min mutuncina matuka gaya, don Allah ku yiwa Aliyu da Sa'adatu adalci." Ya fada yana share hawayen da yake zubo mishi. Shiru falon ya dauka. "Ba zan iya sake Sa'adatu ba, domin sun zubda min cikina ita da Abuturab.........(mura ya dame ni baki daya hancina da Idanuna zubda ruwa suke ayi hakuri .....🤧😪😪)08130269641 Top-notch [26/06, 9:43 am] usmanlauratu71: 50...(I am sorry for being jealous. It's just that i'm afraid of losing the best thing to have ever happened to me.😪) "Ciki??!" Bakidaya falon ya dauka, ita kan bata san me ake ciki ba, ware idanu Abuturab yayi kamar zai fashe da kuka, yana kallon ta. Sake kallon Sa'ade. "Kai talaka gyara zancen ka a gaban mai martaba kake, idan aka gano karya ce bulala zaka sha." Gumi ne ya karyo mishi. "Alhaji Sharif d'anka ne?" Mai martaba ya tambayi Baban Abdul. "Eh Allah ya baka nasara." "Taya aka yi gidanka yake ci da wuta baka sani ba?" "A gafarce ni, tuba nake sai da na tambaye shi, amma ya ce tana son shi, Hakazalika mahaifinta ya tabbatar min da tana son Abdul wallahi ban san sun gaya mishi nima akan nima aka yi ba, da na dakatar da shi." Mai da hankali Mai martaba yayi kan Sa'ade da fuskarta ya tashi. "Malam Abdul, ita mace ba a mata dole a zauna da ita matukar bata so, kace sun zubda maka cikin ka ko? Me ya same fuskar ta?" Ya fada yana tsare shi da idanun, d'ago kai yayi zai magana kamar wanda aka tura mishi sakon ya fadi duk abin da yake faruwa ya kuwa fara bayani. Sai da ya gama tass. Mai Martaba ya ce. "ina son ganin Hajiya Daulah!" "In sha Allah zata zo yanzu." "Allah ya baka nasara don Allah a bani matata " fita Dr Sharif yayi, haka Abdul ya cigaba da magiya har da kuka. Babu wanda ya ce mishi cikanka. Har kusan minti Talatin da biyar, sannan Hajiya Daulah da Dr suka iso. "Ranki shi dade sai yanzu kika zo?" Mai martaba ya tambaye ta, dake mutum ne me yawan fara'a. Kasa tayi da kanta, Ra'is da yake can gefen Abuturab ya komq kamar maraya. Murmushi yana faɗin. "Hajiya Daulah kenan" kasa ƙasa yadda iya Abuturab ne yake iya jin su. "A gafarce ni, tuba nake ina asibiti ne an kai Y'ata haihuwa shi yasa ban karaso ba, tuba nake." "Uzuri ta amsu." Da wutsiyar ido ya kalli yadda Abuturab ya zuba tagumi. "Abuturab me yasa ka ɗauke matar aure bayan kasan ba muharaman ka ba ce?" Gyara zama yayi, domin a rude yake. "Abba yadda Hajiya Daulah take yunkurin cutar da ita ne yasa na tawo da ita Ingila, ban mata kome ba, sai asibitin da na kaita aka duba kunnen ga takardun nan" ya ajiye a tsakiyar falon. Shiru falon ya dauka, sannan ya kalli Hajiya Daulah ya ce mata. "Hajiya Daulah Abdulhakim bakasanmatsi, ko?" Gyada kai tayi sannan ya cigaba da cewa. "Mahaifinki mutumin kirki ne Allah ya masa rahama, mutum ne mai taimakon talakawa. Me yasa baki yi koyi da halin sa ba? Me yasa kika wulakanta wad'annan bayin Allah? Shin idan kika mutu za a binne ki da dukiyar ce? Ko kina da tabbacin duniyar zata cigaba da zama dake? Bayan baki da tabbacin d'anki ya mutu ko yana raye? Sannan ki duba wadannan bayin Allah ki tozarta su zaki ji dadin idan aka miki makamancin haka? " Girgiza kai tayi, ya sake murmushi sannan ya cigaba da cewa. "Waye ya iya magana da ita Sa'adatu?" "Allah ya baka nasara ta iya rubutu?" "Ku ba ni pen da book" mika mishi. Kiranta yayi da hannu, ta matsa a hankali. *Me ya same ki?" Ya rubuta yana me tura mata. Kanta a sunkuye ta rubuta. _Babu kome_ jikinta yana rawa. "Abdulhakim me ka ka mata?" "Allah ya baka nasara, kishi da fushi ne yasa ni dukanta. A gafarce ni"wani irin dunkule hannun Abuturab yayi Sadeeq ya shiga lallaba shi, yana calming dinsa. "A matsayin ka na me niman soyayyar mace ya dace kayi duka?" "Allah ya kiya she mu aikin danasani tuba nake " *kina son zama da Abdul Hakim?* A razane ta d'ago kai, tare da fashewa da kuka. Tana girgiza kai _Don Allah ayi hakuri kar ku kuma, barin shi ya tafi da ni_ "Abdul ga dai abin da tace, Alkali na gama nawa kayi na ka sai na karasa sauran" "Na gode Allah ya baka nasara. Kamar yadda kowa ya sani haramun ne nima akan nima, Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, ya ce na hane ku da ciniki akan ciniki, dan haka Malam dayawan sun yi fashin bakin akan cewa niman aure ya shiga cikin wannan hanin." Nan ya shiga jawo musu aya da hadisai, kafin ya dire da cewa. "Zamu warware auren ka, domin da ace Aliyu baya nan ne zamu iya yarda sannan ko bayan ya saka niman shi bai dawo ba, har ta gama makaranta zamu iya cewa za a warware wancan maganar, sannan kowa yasan ai anyi alkawarin sai ta gama makaranta za ayi maganar auren haka yana nufin kaso kanka domin da ka hakura ka jira Aliyu har ya wuce wa'adin da ya diba ko ina ka shiga kana da damar aurenta. Na farko kun kashe mata mafarkin ta, na biyu kun cutar da ita ta hanyar mata kage da kazafin kisan kai,.na uku Mahaifiyar ka ta wulakantata iyayenta, na huɗu cin zarafin ta tare da dukarta mace, bata cancanci tozartawa ba, idan muka duba yadda Manzon Allah da musulunci suka basu karya, don haka a gaban kowa da kowa Ni Bilyaminu Ahmad babban alkalin kotun Muslunci na majastiri na daya, na yanke hukuncin datse auren Abdulhakim Sharif Hamidu, da Sa'adatu Aminu Fulani. Saki biyu, sannan na soke niman da Aliyu Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari, yanzu Sa'adatu tana da ikon nimawa kanta abokin rayuwar da ya dace da ita, sannan ina me bawa dangin Sa'adatu shawaran su mai da ita makaranta saboda laluran ta, dole sai da Ilimi zata iya daukar duk wani abu na rayuwa, sannan ina mai bawa iyayen Sa'adatu hakuri a bisa abin da Abdul yayi, sannan ina gargadin Abdul da Mahaifiyar sa, da su guji abin da zai saka a kawo su kotu ko kuma gana mai martaba domin haduwar mu ba zata yi kyau ba, idan Sa'adatu ta gama idda zaku iya gwabza niman soyayyar ta, kuma kar wani ya dauki wani abu da sunan niman tilastawa iyayen, kofa a bude take ga iyayen Sa'ade idan aka ga abin da maza biyun suka yi bai da ce na gama nawa Mai martaba." "Madalla, ina ma bawa Iyayen Sa'ade hakuri da abin da ya faru Allah ya kara muku hakuri " inji Dr Sharif, kuka Abdul yake kamar zai cire ransa yana kallon an raba shi da ita, Abuturab kuwa ya ma fi shi shiga damuwa, domin dakyar yake jan numfashi, kirjin shi yayi nauyi. Nasiha Mai martaba yayi musu, sannan aka sallame su. Kowa ya tashi ban da Mutane uku, Abdul da Abuturab sai Sa'ade da take gaban Mai Martaba, bayan Alkali ya mika mata takardan sakinta, bata san meye ba, amma kuma baki daya ta shiga kunci da damuwa, kuka take tana me rike takardan. Matsowa Abuturab yayi ya zauna a gefenta. Suna fuskantar mai Martaba, a hankali ta daura kanta a kafad'ar shi tana kuka. Dawowa gefenta a Abdul yayi ya rike hannunta. Dariya suka bawa mai martaba ya zuba musu idanu. A kasan ransa ya ce. *the worse love triangle* duk abin da Abdul yayi, duk akan so ne, amma bai san yadda zai kyautatta soyayyar shi ba, shi kuma Aliyu yayi kokarin sa ne na a matsayin masoyin gaskiya na ba zan tab'a barin ki cikin matsala ba. Kowannen su yana da muhimmanci da rawan da zai iya takawa. "Ku kyale yar mutane ku bacce min da gani kartin banza" haka suka mike. Haka suka mike kuwa zasu fita. "Abuturab!" "Na'am!" Ya dawo ya zauna yana kallon Sa'ade da take ta kuka har lokacin. "Da alamu kuka zaka min ko?" D'aga kansa yayi sama sannan ya ce. "Allah ya baka nasara ba kuka zan yi ba, kawai Lucky ce take bani tausayi, ita da zata yi murna sai take kuka. She deserves to be happy, but take kuka? Idan shi take bukata mai sauki ne ta koma gare shi amma she is killing me da wannan kukan nata." "Be strong enough mana, ko an ce maka shi na shiri zai yi ba, yaushe zaka koma Ingila?" "Nan da wata uku " "a cikin wata uku ka nimo soyayyarta i promise you zan nima maka aurenta for the second time!" "Thank you Abba" "Allah ya muku albarka " ya fada yana me sallmar shi, itama Sa'adatu rarrashinta yayi sannan ya ce ta je. Haka ta mike ta fita a can waje kuwa drama ake bugawa. "Abba don Allah ka dawo min da Sa'adatu!" Ra'is da Allah ya daura mishi niman fada ya ce mishi. "Yaro kaci karya ka kwana da yunwa a cikin maneman Sa'ade har da dan kwalisa irina, kai kuma you loss your opportunity." "Kai kasan wacece ni kuma kasan abin da zan iya dole na dawo maka da Matar ka" cikin shakiyanci Ra'is ya ce. "Kai kasan wacece Ita? Mahaifiyar ka ce attajiran bogi," "sai naci mutuncin ka" shi kuwa dake dan iya ne yayi ta manna mata Hauka. Jiki a mace ya fito yana kallon su can Sa'ade ta fito tana kallon shi. A haka suka jera har inda ake ta rigima da Hajiya Daula. Motar su Sadeeq Inna suka shiga. Abuturab ya bude mata baya ta zauna. Hawaye ya zubo mata tana gogewa da bayan hannunta. Dauke kai Abuturab yayi, yana tsaye suka tafi. "Man kayi kokarin niman mafita kafin ku koma london." "Bani da wannan kwarin gwiwan" ya fada yana kallon motar har ta bar gidan. Haka suka koma cikin gidan, dakyar yayi barci ya dauke shi. Da sassafe suna tashi sai Kwara. .... Itama Sa'adatu Inna tana lura da ita yadda ta gigice, kuka take lokaci zuwa lokaci. Duk da bata son auren amma Mutuwar auren ya dake ta. Har dare ya raba Idanunta biyu, tashi Inna tayi ta gabatar da alola tazo ta gabatar da sallah nafilla. Sai asuba ta koma barci, Washi gari ta tashi da ciwon kai me zafi. Sannan ta yi wanka tare da gyara dakin. Abin karyaawa suka fita yi wurin Aunty Ummy. Bayan sun gama ta kawo nasu Inna. Ƙwanciyar ta tai. Har barci ya fara daukar taga mutum a kanta. Bude idanu tai Husnah wani irin dira tayi a gadon suka rungume juna. Sai kuka kamar me. Sai da suka yi kukan ya ishe su, sannan suka shiga hira da abin da ya faru, Husnah ta tausaya mata. Sai can yamma sannan Husnah ta bar gidan, har dare babu Aliyu babu me kama da shi, duk abin duniya ya dame ta. Har dare babu al'amar sa. *** Kwara Sun isa lafiya, sai hidima Ummi take mishi ga wanda yan aiki suke masa, gwanin ban sha'awa. Suna tsaka da cikin abinci Sarah ta shigo. "Prince yaushe ka iso" kallonta yayi na wani lokaci kafin ya ce mata. "Dazu!" "Queen Mother shi ne ba a gaya min na?" Daure fuska yayi ya ce mata. "Ummina ce zata gaya Miki na iso?" "No ba haka nake nufi ba, but Queen Mother." Tausayi take bawa Ummi tun ranar da abin ya faru, ake gulmace-gulmacen ta samu tab'in hankali domin tayi sati daya ba a ganinta. A karshe aka fara surutun ta zare, sai tayi ta abu kamar mahaukaciya. "Sarah " aka kira ta daga waje, mikewa tayi ta mika mishi wani hanky tana washe baki. Amsa yayi ya ce mata. "Nawa ne?" Gyada kai tayi tana dariya ta ce mishi. "Bari nayi gulmarka wurin Queen Mother " zuwa tayi daidai kunnen Ummi ta ce mata. "Queen Mother akwai turaren da ake sakawa ki ce kar ya shaƙi iskar turaren...........🧟yar macukule zata ballo Agustan.....08130269641(Ni kan daga yau na tafi hutun sallah sai kuma monday in sha Allah... Mu hadu.....Nagode da Addu'oin ku👏✨ [29/06, 8:03 am] usmanlauratu71: 51...........Hajiya kina sana'a? Ko dai Haka kike zaune Allah ya Baku mu samu?🤣 To Bari na Baki labarin resin art! Nasan kwana biyu kina ta ganin shi a WhatsApp story din mutane. Resin art digital course ne da zai Baki life time skills🥳 I repeat lifetime skills, in da Zaki iya yin designing Dan kunne, key holders, gifts da abubuwa da dama, how I wish Zan iya hada muku hoto ku gani. Da naira dubu ashirin da biyar wato N25,000 only zai Baki access to course din, Kuma Ina tabbatar Miki cikin kankanin lokaci kin maida kudin ki. Domin Karin bayani, tuntubi wannan contact din akan WhatsApp! 08034174725 "Ki kore shi maza ya bar gidan nan idan ba haka ba, zasu shaka mishi iskar domin da .." "Sarah" Abdulrashid ya kwala mata kira, "na'am, na haukata kaina ne domin na gaya miki gaskiya. Ki saka a bincika miki ga shi nan" ta ciro kulli a cikin aljuhun rigarta ta mikawa Ummi. "Idan na shigo sai na balla miki kafa." "Prince ka aure ni kaji, domin da na jikinka za a iya kashe ka, amma ga wanda yake da kyakyawar manufa za a sha wuyar kashe ka." Ta fita da gudu. Bin bayan ta yayi da idanu. "Ka fahimci me take nufi?" "A'a" buga mishi pillow Ummi tayi. "Me yasa baka ganewa ne?" "Zaki gane sai lokacin yayi ni dai ki saka baki a ba ni auren ta." Irin ta nuna mishi abin da yake na rashin damuwa da kome ta ce mishi."Sarah?" " Kai haba murus zata saka a cinye ni" "ai kuwa zata dace da kai" ture bowl din gabansa yayi ya gyara zama. "Ummiiiiiiii" "Na'am dan lele na!" "Lucky I meant." "Hmmm! Yarinyar da bata gama makaranta ba?" "Zan tsaya tayi karatu in sha Allah " "maza haka kuke da dadin baki, ban yarda ba" "Na rantse zata yi karatu" "hmm haka kace, kayi lissafin mana, ana baka ita, sai ciki sai renon ciki, bayan haihuwa sai renon d'a haba shekarun ta nawa ne haka?" "15yrs da watanin." "Kai subhanalillahi yar karamar yarinya zan baka?" Tattaro hankalinsa yayi ya zuba mata ido. "Ummi baki damu da ni ba ne?" "Na damu da kai, amma ba yana nufin zan dauki yar mutane na baka ita babu ilimin rayuwa ba, sannan tsakani da Allah tayi karama." Ta fada cikin kulawa. "Amma ni sai nake ganin auren shi ne mafi alkhairi, haihuwa da reno shi kuma wannan sha'anin Ubangiji ne a bar masa kayansa, idan kika ce kar ka na auri lucky ni me biyayya ne, kuma ba zan kuma miki maganar ta ba, amma har ga Allah na cutu dayawa. Zan iya biyayya na rike matar da bana so amma zan yi bakin ciki hana ni matar da nake daidaita da rayuwata. Ki huta lafiya." Ya mike zai bar falon, "zo nan baba ubana!" Tawowa yayi ta bude mishi hannu. Dan daidaita kansa yayi ya ɗan rungume ta, sannan ya sake ta. "Na rigada nayi yanke hukunci, ba zaka auri Lucky ba sai na duba dangantakar da yake tsakanin su." "Shi kenan Ummi." Tana jin yadda muryan shi yake rawa. Baki daya sangarta ya gama bata mishi rayuwa, a gaban mutane yake Strong Man, a gaban Umminsa wani irin rikitaccen yaro ne da bai da mara ba da d'an yaye. Share shi tayi ta ga iya gudun ruwansa. Akwai abubuwan da dole yasa ta kalle su kafin tayi maganar auren shi da Sa'ade. Na farko gidan su babban gida da dole iyawa ruwa fida kai ne. Na farko kenan, sannan tasan nesa ba kusa ba, ba zata iya goga kishi da Latifah ba, domin bakin rijiya ba wurin wasan Yaro ba ne. Na uku tana shiga idan ba Allah ya kawo mata hutu ba, ciki zata yi karshe ta zauna rayuwarta babu cigaba sai, daga aure sai haihuwa sai renon yara. Babu abin dazata nunawa kishiya. Koda zata bashi damar auren Sa'ade to kuwa yarinyar ta san darajar kanta. Tana son ta zama me kwatar kanta a kowani irin yanayi ba a mata auren da zata kasa amfanar kanta balle kuma shi kansa bai da ikon kare ta daga sharrin gidan da yake ciki ba. Ina ya gama fushin sa zai hakura ya fahimci abin da take nufi, saboda son ransa ba zata iya cutar da yar wasu ba, ai shi ma yasan dai haka ba zai yiwu ba, duk abin da zai yi sai dai yayi amma taya zata goya masa baya ya dauko yar mitsisiyar 'ya da sunan ta goya mishi baya ya aure ta. Idan su iyayenta basu da lissafi ita nata lissafin a cike yake tam, bata iyawa da fitinar masarautar nan, yanzu a fara yawo da ita zata take hakkin yarinya karama ko kuma su ce an sayo ta da kudi, duk da ba sabon abu ba ne, bata mantawa lokacin giyar hauka tana kwasar Abuturab da Mansurah har cewa aka yi ita ta daure musu gindin suke aikata abin da suka so tunda har zuwa aka yi aka gayawa Sultanate da Uban Mansurah cewa ai Abuturab ya gama lalata mishi 'ya kuma ita ba zata tab'a barin D'anta ya auri Mansurah ba, wannan sharrin sai da ya sa ta mari Abuturab, domin kuwa ana cikin wannan case kawai kamar ance ta je dakinsa, ta same su suna kiss din juna, kuma abin da ya fara zuwa ranta ba yau suka fara cinye bakin juna ba, haka yasa hankalin ta yayi mugun tashi wanda yasa karshe sai da ta kwad'a mishi mari, tayi fushi sosai da shi. Ita kuma Mansurah ta dauke ta, zuwa asibiti aka duba mata ita ko ya shiga jikinta. A lokacin da Likitar ta gama binciken tana murmushi sai da gabanta ya fadi domin ta zata abubuwan sun wuce saninta ne, sai gashi tana cewa. "Maam lafiyar Yarki kalau, babu abin da ya samu wurin." Ta jima tana mata bayani sannan Ummi ta gamsu domin gani take Abuturab ya lalata musu Y'a kamar yadda take zato. Shi yasa a lokacin tayi ya kaf-kaf da ita domin kar wani abu ya fada tsakaninsu tow gashi Allah ya da ikonsa shi bai yi abin da ake zato ba wasu sun yi har anso a daura mishi sharrin da bai aikata. Don haka ba zata tsaya a bashi Sa'ade yazo kwana biyu yana rena mata hankali ba, domin tasan halin yan maza, yanzu zasuwa mace abu a baki sai ta ji dadinsa sai su cire abinsu. Don haka ta ce bari.ta zuba mishi ido taga gudun ruwansa. Ai kuwa kusan kwana biyu bata saka shi a idanu ba, gefe daya ta sha'afa da zancen Sarah, *** Abdul. Tun ranar da aka ce an soke auren shi da Sa'ade. Ya kwanta rashin lafiya domin sai yanzu yake jin masifar kaunar Sa'ade, ya kauracewa gidan iyayensa, duk kiran da Aunty Fareedah, hankalin mahaifiyarsa tayi matukar tashi domin shi ne karfin ta, haka tayi ta zarya daga gidansa zuwa gidanta. Abin tambaya anan shi ne dama tana son farincikinsa ta hana shi nutsu da matar da yake? Domin kuwa baki daya Abdul ya mata duk abin yake so me yasa ita bata bashi abin da yake ba? Tayi ta kalubalentar matar da yake so, ita sai yanzu take mugun aikin da ya aikata, me yasa bata yi tunanin bar shi da matar sa ba, tayi ta d'aga hankalin ta sai ya rabu da yarinyar. And shima yayi laifi me yasa ya tursasawa yarinya aka mata auren dole? Bayan san bata son shi, ai idan duniya da gaskiya sai ya nime soyayyar ta, amma sai ya zaga ya lalata goben yarinyar yadda ba zata iya amfanar kanta da wuri haka ba, gashi sun yi biyu babu, shi ba ga mata ba ita ba ga danta ba, baki daya abin ya zame mata wani iri, tunda abin ya fara jininta ya haura dari da wani abu, gashi yanzu ko Taufik baya kwanan gidan, balle ya binciko mata halin da dan uwansa yake ciki. Ta kira Saddikah ta gaya mata, cewa tayi babu ruwanta ai tun farko ta ce ta bar mishi matarsa amma taki gane abin da take nufi, ai ga abin da ya faru. Ita don Allah ta rufa mata asiri kar ta lalata mata rayuwar auren ta domin ta lura abin da tayiwa Abdul ya janyo mata gori a wurin kishiyarta. Dan abu ba abu ba sai gori da habaici..... (Barka da Sallah a ci nama a hankali fa) 08130269641 kuyi hakuri babu yawa [02/07, 1:51 pm] usmanlauratu71: 52...........Hajiya kina sana'a? Ko dai Haka kike zaune Allah ya Baku mu samu?🤣 To Bari na Baki labarin resin art! Nasan kwana biyu kina ta ganin shi a WhatsApp story din mutane. Resin art digital course ne da zai Baki life time skills🥳 I repeat lifetime skills, in da Zaki iya yin designing Dan kunne, key holders, gifts da abubuwa da dama, how I wish Zan iya hada muku hoto ku gani. Da naira dubu ashirin da biyar wato N25,000 only zai Baki access to course din, Kuma Ina tabbatar Miki cikin kankanin lokaci kin maida kudin ki. Domin Karin bayani, tuntubi wannan contact din akan WhatsApp! 08034174725 *BARKA DA SALLAH mutanen Hajiya Daulah kun san wace ce Daulah?🤣😹* Confessing.... Diddin walahairan Hajiya Daulah tana hanyar gidan Abdul amma fir yaki fitowa, asalima rufe gidan yayi ya hana a barta shigowa. A yammacin kwana bakwai da rufawan al'amarin ya shirya cikin wani boyel sky blue. Sai hular zanna bukar da ya murza da takalmi hafcover. Yayinda ya wanke jikinsa da turare mai kamshin tsiya. Duk inda ya wuce sai kasan ya wuce. Yana fitowa ya dauki key motar shi, ya nufi hanyar unguwar su Sa'ade. Koda ya isa ya samu Baffa a waje yana shan iska. Ji yake kamar yaje ya rufe tsohon nan da duka, amma kuma yasan babu halin haka. Sa'a yazo gani, idan ba ita ba wace ce zata kawo shi nan? Fitowa yayi daga cikin motar ya nufi kofar gidan, har kasa ya gaida Baffa, kasan a kasa ya gaza mikewa balle har ya fahimci irin kallon da Baffa yake mishi. "Shin na tambaye ka, me ya kawo ka kuma yanzu?" "Na zo wurin Sa'adatu ne!" Ya furta muryan shi tana rawa, yadda yayi maganar tausayi ya bawa Baffa, yayi shiru kafin ya mike tare da buɗe mishi kofar dakin sa na waje. Suka shiga sannan ya zauna yana kallon yadda Abdul ya takure a wurin guda. " Me yasa ka dake ta bayan kana sonta? Ita mace irin ta rarrashinta ake ba uzura mata ba, duk yadda nake son abin duniya ina sonta itama baka tab'a nazarin haka ba ne? Aure rai ne da shi, a lokacin da Alkali ya raba ku na tausaya mata domin har muka dawo kuka take. Sai dai haka ba yana nufin kukan rabuwa da kai ba ne, tana yi ne domin gajiya da rigimar da ta shiga, idan har Sa'adena matar kace har abada, duk kiyayyar mu ba zamu tab'a iya hana ikon Allah ba, jeka ka nime soyayyar ta a karo na biyu. Amma ka sani akwai Aliyu ba zan iya cewa ya fika ba ko ka fishi ba, ku gwada irin taku baiwar akan macen da kuke so ko Allah zai baku sa'a. Bari na kirawo maka ita." Fita Baffan Sa'ade yayi, baki daya jikin Abdul ya mutu, yana nazarin maganar gaskiya da Baffan Sa'ade ya gaya mishi babu karya ko son rai iya gaskiyar ce mara algus. A can cikin gidan kuwa, tana kwance kanta bisa cinyar Inna, "Assalamu alaikum, Laminde bani aron Yarki Abdul yazo ne!" Kura mishi idanu tayi kafin ta ce mishi. "Babu inda zata, ai dama nasan halinka ana baka kudi tuni zaka manta da wani wulakancin da aka maka, amma ka sake kwaso dan attajiran duniya?" Murmushi yake yayi sannan ya ce mata. "Ki bar fadar haka idan Allah ya nufa." "Bama zai nufa ba." Ta fada tana kauda kanta can gefe."toh naji taimaka min ki sata ta saka mayafinta taje ina ga yazo niman yafiyarta." Babu yadda ta iya haka ta saka Sa'ade shiryawa ta fito, suka nufi falon. Tana ganin shi ta ja da baya kamar zata juya a guje. Girgiza mata kai Baffanta yayi yana rike hannunta, har cikin falon ya ajiye ta, sannan ya saka kai ya fita, mannewa tayi a jikin bango tana kuka. Takowa yayi ya iso gabanta, ya riko hannunta. Rintsa idanun tayi tana jin kamar wuta ake d'aud'ana mata, zare hannunta tayi, kura mata idanu yayi yana jin saukar hawayenta kamar ana zuga mishi yake ji, janyota yayi ya rungume ta."I'm sorry" ya furta a saman kunnenta, sake rungume tayi kam'kam yana jin wani irin yanayi, wanda yafi karfin ya kira shi Feelings or desires, pure love ce a tayi masifar danne wadancan abin da yake ji, shafa bayan ta yake a hankali domin yana jin kukanta har cikin ransa, bai fasa rarrashi loln ta ba, yasan yayi mistake amma kuma zai iya gyarawa domin ya same ta a second chance. Baya jin zai iya rabuwa da ita gara ya ga mutuwar sa da ya rasa ta. Wannan shi ne alkawarin da yayiwa kansa. D'ago kanta yayi da niyyar kiss din, ta juyar da kanta jikinta yana rawa. Karshe kifa kanta tayi a kirjin sa. Duk yadda yaso ya samu damar sumbatar ta. Amma yarinyar nan taki haka ya hakura ya d'ago hannunta ya saka a kan kirjinsa. D'ago idanu tayi tana kallon shi. Ya nuna kansa sannan ya nuna ta, kafin ya d'ago daya hannun ya haɗa da nashi, yayi shap din luv, "ina sonki" hawaye ne ya zubo mishi, "ina sonk" sake kai hannun shi yayi fuskarta. "Ina sonki, kuma zan yi fada domin na rayu dake, koda zan mutu zan mutu dake ne, Sa'ah ina sonki" Sunkuyar da kai tayi, sannan ta juya zata fita ya riko hannunta. A hankali ya rungume ta, tana jin yadda hawayensa yake zuba a bayan ta. Sam bata wani shaukin so akan sa shi yasa take ganin haka a matsayin damuwar da ya daurawa kansa, haka ya gama shiririntan sa ya kyaleta. Haka suka rabu dutse a hannun riga, a haka lokaci ya cigaba da tafiya har an samu tsawon Wata guda, amma babu ranar da gari zai waye Abdul bai zo gidan ba, tun Inna tana jin haushinsa har ta hakura ta zuba mishi idanu, wani irin mahaukacin so yake nunawa Sa'ade, idan yana gidan tana daki. Idan kuwa ya zo ya samu tana waje tana aiki a tare zasu gama aikin, duk da gargadin da Alkali ya mishi, haka bai saka ya fasa zuwa ba, duk zuwan da yake Zakaria bai sani ba, sai a ranar wata Laraba, yayi mantawa ya zo gidan domin daukar abin, shi ne ya so ya samu Sa'ade na wanki shi kuma yana dauraye mata kayan, abin ya bashi mamaki. Riko wuyar rigar shi yayi ya ja shi har waje. "Uban waye ya baka izinin zuwa wurin kanwata?" "Ina son mata ta, kuma zan gyara kuskure na, ka bar ni na gyara kuskure na" a fusace Zakaria ya ce. "Har abada ba zaka tab'a samunta ba, ka wuce kafin na lakad'a maka duka" "zan yi fatan haka, matukar haka zai sanya Sa'adatu ta dawo gare ni ba zan yi fushi ba." Tsaki Zakaria yayi ya koma. ya fara masifa har da matar shi da bata san kome ba, ya haɗa da ita. "Bar masifa Baffanku zaka samu shi ya sahale mishi yake shigowa, bayan haka babu yadda muka iya da shi, wuka da nama yana hannun Sa'ade idan taga zata iya oho manta idan kuma zata jira Aliyu ne ina mata fatan Alkhairi shi yafi cancanta sa ita sama da wannan Yaron da uwarsa bata da mutunci ko kaɗan." "Kar ya kuma shigowa cikin gidan nan, ya je can ya karaci haukarsa" *** Kwara. Tsawon wata guda Abuturab ya dauka yana yaji, yo watsar da shi Ummi tayi, domin taji labarin yadda suka yi a sokoto, a bakin Ra'is. Don haka ta zuba masa na mujiya, kuma abin dariya sai ya gama gudun sa cikin dare ya tattaro falonta na sama ya kwana, idan abinci ne ita da kanta take ajiye mishi a sama domin akwai mini kitchen a saman, tana jin motsinsaa bata wani damu ba, yau tun safe take hankoron ritsa shi. Aikuwa ta sauko har dakin sa yana banɗaki, kan gadon sa ya baza wasu takardu ne yayi rubutu a kai, tare da wasu abubuwa da alamu bincike ne na fitar hankali yake. A hankali ta kai hannu zata dauki wasu fararren takardu, ya fito." Ummi haramun ne bincike fa, d'aga hannun tayi ta nai kan passport din Sa'ade. D'aga takardan da passport din Sa'ade yake tayi hotonta ne, a hankali ta shiga bin hotunan gadon tana buɗewa ta kai hannu zata bude na ƙarshe, ya rike hannunta. "Kiyi hakuri wannan aiki na ne." "Me yasa kake cusa kanka cikin hatsari?" A hankali ya zaga ta, ya dauke hoton ya bude mata jikin bangon da ya saka labule ya rufe, taswirar masarautar ce, tare da hotunan su. "Abuturab!" Towel ya dauka yana goge kansa. "Sannan ya dauki hoton duk wanda ta bude yana mannawa da sunansa, a hankali ya gama sannan ya dauki hoton sa Sa'ade ya saka a tsakanin hotunan. "Wetness ce, domin an kawo mata hari a london muna tare, idan har yadda nake tsammanin ne, Latifa ita ce take bada information a kaina, sannan mutuwar Abubakar tana da saka hannu a cikin sa." "Yar dan uwana ba zata aikata haka.ba" murmushi yayi ya rungume hannunsa a kirjinsa ya ce. "Me yasa kike tunanin ba zata yi haka? Ni kuwa ko waye ya kusance ni ina sane da shi. Kinga wannan yarinyar dole na aure ta, domin ita ce kaɗai ba zata iya kashe ni ba" ya saka marker a saman hoton Sa'ade. "Ko ban aure ya don kome ba, xan aure ta domin ina Kaunarta." Ya wuce da hoton hannunsa, idan ga ga hoton faduwa zata yi ta mutu, hoton Jalilah da hoton Zuwairah, sai saman can hotunan Sultanate ce sai na Sultan. Dawlat khatoon da danta Muhammad, wanda baki daya ya saka musu arrow akan hoton Sultanate, kasa kuwa hoton Sultan Abdulsamad ne, sai kasa hoton Abdulrashid, kafin hoton Mansurah da mahaifinta wanda aka saka hoton Ummi ya saka mata arrow. "Me yasa har da hotona" "Idan har soyayyar da zata zama mafi girma da tarihi, baki tunanin kiyayyar da zata iya rikidewar abubuwa guda biyu nan?" "Me ya kawo hotonan Addahta?" "Domin ita ce mutum na biyu da aka fara kashewa sai Hamma Muhammad, kafin nan. Kai Ummi jeki duba " "tsoro nake ji kar zuciyata ta buga " shiru yayi, kwasar kayansa yayi ya shiga ban daki tana tsaye yana kallon hotunan tana son gano bakin zare guda ɗaya amma ta kasa. "Ummina ya dauke ni shekaru hudu zuwa biyar ina nazarta criminalogy, yadda masu laifi ke da nasaba da juna. Ummi idan nace miki wani abu akan wannan laifin hala tarewa zaki yi a asibiti." "Tunda kasan wani abu dole a kira Sultan ya sani." ta juya zata fita. Riko hannunta yayi ya zauna da ita a bakin gadon ya durkusa a gaban ta. "Idan baka iya kama barawo ba, tsaf zai kama ka Idan kina son kama su dumu - dumu dole, ki tafi a yadda suke. " Janyo drower gadon yayi ya cire wani takarda ya mika mata da wani karamin kwali, " wannan turaren wutar da Sarah ta gaya miki, wannan kuma hmm karki bude takardan domin garin sinadarin kulorin ne, tacce ruwa ake da shi idan za a sake shi a cikin gari, yana kashe ƙwayoyin halittar ruwa, amma shi ayi ta zubawa Hamma yana sha a shayi. Hajiya ban gama bincike ba, don haka ki bar zancen zaki gana da Mijinki domin ba yarda za yi ba, kema idan na gaya miki gaskiyar da nake boye miki hala cewa zaki yi gara ki mutu kawai." Ya tashi zai fita ta ce mishi. "Yanzu me kake so?" "Lucky " juyawa tayi ta hango bala'in da ya shirya ta ce mishi. "Ba zan iya baka ita ba" agogon hannun shi ya saka yana faɗin. "Nan da wata biyu zan koma da ita london a mata aikin kunnenta Latifa ta mai da ni wawa wai ta sama mata school, ki nima min auren." Ya tsuke fuskar ta ce mishi. "Ina matarka " janyo stool yayi ya zauna ya ce mata. "Ummina bari na gaya miki gaskiya ba zan iya zama da ita ba, asalima babu abin da ya haɗa ni da ita wallahi kawai aure ne ke kika kulla kuma ko yanzu zan iya sake miki kayanki." "Abuturab ban gane ba" Mikewa yayi yana faɗin. "Ki saka baki kawai a bani Lucky, ba zan hanata cigaba ba, domin wallahi na tafi da ita babu aurena kanta zan je can na daura auren sai dai mu dawo miki da jika, iya gaskiyar kenan ina son abata." "Ni kake gayawa zaka aureta a can?" "Ummina gaskiya na gaya miki, wallahi iya hakurin da nake ya wuce yadda kike tunani, idan baki sonta zan hakura idan kuma kina ganin lafiya lau ce, tow wallahi idan na d'auketa zan yi kome Allah ya gani na gaji a bani damar zama da ita." "Idan ban baka damar auren ta ba me zaka yi?" Juyawa yayi a sakalce ya ce mata. "Na rantse, dauke ta zanyi na mata abin." "Aliyou!....... 1=400 2=800 3=1000 08130269641 [03/07, 10:38 am] usmanlauratu71: Mother's Love..... She is my daughter not my In-law. 53...... "Ummina ai gaskiya na gaya miki!" "Aliyou yaushe na zama abokiyar wasarka?" Murmushi yayi ya ce mata, "Kin koya min fadar gaskiya a duk inda, taya kike tunanin zan fada miki akasanin haka? Wallahi Ummina matukar baki shiga lamarin, Allah zamu tara yara a waje domin na tafi da ita, ba zan iya hakuri na zauna da ita...."D'aga hannu tayi alamar ya isa haka, sannan ta gotta ta gefen shi zata wuce. "Ba hanaka ita nayi ba, sannan saboda son rai, ba zan baka damar aurenta ba, tayi kankanta da ɗaukar kome, bata san damuwa ba sai bayan haduwar ta da mijinta, taya kake ganin zata zo nan ta kwaci kanta? Look Aliyou ba fa hana ka zan yi ba, ni da kaina na maka alƙawarin Nima maka aurenta, amma dole sai mun fita a wannan yanayin. " Zubewa yayi a kan gwiwarsa. Ya rike hannun ta, "ki ajiye yanayin da kike tsannanta min, ki bani damar aurenta, koda ba zata tare ba na amince amma matukar na bar kasar nan da ita, zan haukace akan ta. Wallahi Ummi tsawon shekaru talatin da wani abu ina gudun Zina a yau ma nasan ina gudun ta, sai dai hanyar da zan bi da ita ba zan iya hana kaina ba. Ummina ni d'anki ne, don Allah ki bani damar nutsuwa da ita, wallahi zata yi karatu har sai ta gaji, idan har Auren Abba da Yara bai hanaki karatu ba, akan me zan hanata?" Yadda yaƙe maganar gaskiya sai da ya tab'a mata zuciya, amma taya zata sahale mishi auren Sa'ade yarinyar da ko secondary school bata gama ba, tasan su waye mazan masarautar, duk macen da zasu haɗa shimfida da ita an gama magana, matukar lafiyayya ce rabo me tsanani ke shiga tsakanin su. "Aliyou ni da ita akwai banbanci, ita yarinya ce da bata ji ko magana, idan ka lura akwai cutarwa. Taya zan fahimtar da kai?" "Izuwa yanzu ya fara fahimtar Umminsa ba zata tab'a barin ya auri Sa'ade ba, don haka ya mike bai ce mata kome ba, ya shige dakinsa ya rufe kofar. Rub da ciki ya kwanta, murmushi tayi ta wuce abin ta, tana faɗin. "Zan baka mamaki, ba zan tab'a barin ka min kallon mara adalci da son kai ba, ba dai Sa'adatu sa'ar mata ba ce." Sosai yayi fushi itama ta tattara shi ta watsar, kusan kwana biyar bata yi bikon sa ba, sai da yammacin kwana na shida Sultan Abdulrahman ya shigo sashinta, zama yayi sosai sannan ya kura mata idanu. "Irin wannan kallon ta meye ne?" " Mamakin abin da ya haɗa auta da babarsa." D'ago kai tayi tana kallon shi, kafin ta ce mishi. "Kai karana yayi kenan?" "A'a bance ba Madam, amma kuma ki kyale shi ya auri yarinyar, idan" "Ni fa ban hana shi ba, kawai yarinyar nake son tayi kwari, bayan kasan cewa yanzu sai a fara kananun magana." "Ni kuwa sai nake ganin kamar ai hannun hagu ba bakon wanke kashi ba ne, yau aka fara? Ki bar shi ya aure ta;" "yarinyar kurma ce sannan iya secondary school ma bata gama ba, balle har ayi maganar auren " "Amma ai tayi mu'amalar aure da wani namijin? Baki tunanin yanayin da wancan ya sabar mata yayi affected din ta." Gyara zama tayi ta ce mishi. "Yanzu kan na fahimci abin da Baba karami yake nufi, da ya gaya min haka tun farko ba zan hana shi ba, sai dai ka gaya masa ban yi niyyar ya aure ta ba" da a cigaba da abin take yi. "Badi'atul " "Na'am yallabai!" "Me yasa kike haka ne?" Harara ta watsa mishi. "Bai da wata matar ne?" "Tow amma ita wancan yake so" "tow sai ya jira ta gama makaranta tukun." "Gaskiya babu adalci a wannan lamarin" "kace me?" Domin yayi maganar kasa ƙasa ne, "Allah ya baki lafiya da nisan kwana." Ya fada yana kallon gefe. Shigowa Abuturab yayi ya kalli fuskar Abban su, daga yadda ya zauna ya fahimci babu nasara. Bai ce musu cikanku, kallon shi tayi iyakar tausayi yana bata, amma bata jin zata iya daukar haka a matsayin son zuciya, sai dai zata bashi mamaki. Tashi Sultan yayi ya bar falon, ta dauki wayar ta ta kira dan uwan Mahaifinta. "Sannu Abba" ta fada a hankali. "Abba dama Abuturab ne yake son kara aure, shi ne na ke son gaya maka. " Tasan shi ne kakan Latifah tunda shi ya haifi Kudirat, gyara ta gaya masa domin kar su dauka wani abu take yi, musamman yadda Abban ya dauke ta kamar yarsa ta cikinsa. "Maa sha Allah, Baba karami ya girma, dama ina tason kiranki. Akan maganar baba karami, ko zaki shiga gaba a bashi rikon kwaryar kujeran wazir!" Shiru tayi na wani lokaci kafin ta ce mishi. "Anya baba karami yana karatu, kuma a rayuwar shi babu ra'ayin mulki sai karatu." "Da dai kin duba dai, ai karatun yana da kyau, amma ya kamata a ba shi wani matsayi shi ma." "Tow zan duba." Iya zuwa yau tsoron wani mukami na sarauta take ji, Saraki da Maina tun su na yara ake alakanta sunayen su da sarauta, har zuwa yau da mutuwa ta dauke su, bata da zaci haka ba sai da ta fara binciken files din da aka turo mata ta gane, an kashe mata yara ne domin kawai suna alakanta kansu da wani positions na masarautar, bayan laifin da Sultanate ta aikata, haka kawai a bawa Aliyou matsayin Wazir ai shi kansa mutuwa zai yi be shirya ba, domin baya kaunar matsayin sarautar nan. Su je can su karata. A hankali Abuturab ya fito yana kallon ta. "Ummina da waye kike waya?" "Abba Laminu!" Tab'e baki yayi yana faɗin. "Allah sarki" ya wuce. "Dawo nan baba karami" "tow Ummina" "ba wani umminka kai karata ka kai?" "Hala ya miki fada ko?" Ya tambaye ta a dan rude. Harara ta watsa mishi. "Kaniyar faɗa yayi min! Baba karami kar ka kure ni fa." Sauka yayi a kujeran ya zauna a gabanta. "Ummina ke da kanki kika gaya min illar da zina take da shi. Ummina me yasa ba zaki bar ni na aure ta ba? Ummina ko Mansurah kin ga nayi haka a kanta? Wallahi Ummina akan lucky nake bin ki, idan akan wata ce ba zan ta nacin binki ba. Ummina yarinyar nan ba kwaila ba ce, wallahi ta fi wata yar talatin ma cikar zati " make kanshi tayi. "Baka da kunya ne?" Ta tambaye shi, tura mata baki yayi ya ce mata. "Ina ruwa na da shi, akan matar da nake so na manta akwai wata kunya kawai, Hajiya Ummina ki shiga lamarin." Kura mishi idanu tayi ya ce mishi."Ina son ka koma london idan lokacin aikin yayi zan tura maka ita." "Ummina!" Ya kira sunan ta razane. "Me yasa toh?" "Umarni na baka ka tafi zan nime ka" hawayen b'acin rai ta hango cikin ƙwayar idanun shi, ta dauke kai kamar bata sanin halin da yake ciki ba, idan ta gaya mishi zata tsaya mishi tsaf, zumudi zai saka shi ya nunawa dangin Mahaifin yana son auren, amma idan baya kasar haka zai saka a gane cewa kawai za ayi auren nan ba tare da ya damu da ita ba,sannan ita kanta Latifah zata yarda cewa zai yi adalci. "shi kenan gobe in sha Allah zan wuce." Bata kalle shi ba, ta ce mishi. "Ok Allah ya kai mu" ta cigaba da abin da yake. Tashi yayi kamar zakarar da ruwa ya mishi mugun duka, ya wuce part dinsa. Har dare bata ga wucewar sa ba, sai da ta ga Jalilah da burna ta ce mata. "Me zaki yi da shi?" "Zan saka turaren wuta ne ranki shi dade" tunawa da tayi da zancen Sarah. _Kar ki sake ya shaki hayakin turaren wutan_ "ki bar shi sai gobe yanzu dare yayi." Dake Ummin tana falon. "Tow" ta fada, zata fita. "Muga turaren" "Na'am?!" Ta fada tana me juyawa tana kallon Ummi. "Baki ji bane? Turaren wutar nake nufi" sosa kanta ta fara tana zare idanu. "Ko babu ne a wurinki?" "Eh....eh sai naje ɗakinki na turare na ɗauka." "Ok ba damuwa bar shi kawai" "tow" ta wuce fada sauri zuciyar ta na rawa kamar zai fado waje, yau da an kamata sai na lahira ya fita jin dadi. Murmushi tayi sannan cigaba da lazuminta.ko abinci yau da kanta ta dafa ta kai na Abuturab dakinsa yana shirya kayansa. Ajiye mishi abincin tayi ta ce. "Delicious is ready " ta fita abin ta, tura baki yayi kamar yana gabanta, ya je ya zauna ya fara cikin abincin. Washi gari kuwa da wuri ya bar garin kwara, ya wuce lagos. Hankali ya kwanta sosai domin kuwa shirinta take kafin kowa ya sani. Kuma tasan Abuturab da zumudi idan ya san zata nima mishi auren Sa'ade tsaf, zai iya zuwa can ya tare amma idan ta nima aka aura mishi ita aka tura can sai dai a sha bikin anan sosai zata shirya mishi bikin. Kuma tunda ya rantse da Allah zai zauna da ita zai bata damar tayi karatu zai yi, a karshe ta kore shi domin taga karfin soyayyar da yakewa yarinyar da soyayyar da yake mata, zai yi biyayya ya tafi sai ta ga ya ce tow. Daukar wayar ta tayi ta kira shi. "My boy ka cewa Sa'ade goodbye kuwa?" "Ummina tana idda, duk da nasan Abdul bai isa ya mai da ta ba, amma kuma naso haka, but Allah yasa haka shi ne mafi alkhairi." "My boy Allah ya tsare ka gaida min Latifah kaji Allah ya baka abin da kake so." "Allahumma Amin, Ummina." Murmushi tayi ta ce mishi. "Baka yi fushi da ni ba?" "Akan me Ummina? Nasan kin fini hujja, don haka har abada ba zan yi fushi dake ba, wallahi bana fatan fushi da uwata da tasan darajar D'anta da farincikin sa, duk abin da zaka yi domin gobe na ne, da yakin da yake gaban mu." "Na gode sosai da fahimtar da ka min. Na zata zaka dauke ni a matsayin azzalumar Uwa ce me hana D'anta farincikin rayuwarsa." "Kai Ummina bikona kike kar nayi fushi da ke? Kuma akan Lucky, idan ina tare da ke ina manta wace ce Lucky da duniyar ta, amma idan ina tare da ita kece mace na farko da take gefena, na san kina da reasons masu girma, kuma ina son ki so Sa'ade bana son sanadin soyayyar da nake mata ki tsane ta, ni d'a ne wanda ya girma da soyayyar uwarsa, bana fatan matar da nake so Uwata ta kyamaceta. Domin nasan Uwata she is best Mother." "Allah ya shiga lamarin ka, ya baka sa'a a cikin duk wani lamarinka, ni kuma zan tabbatar maka ni ba uwa ce mara adalci ba, uwa ce da ta rayu tsawon shekaru arba'in da biyar domin kare Yaranta, zan zame maka jar kaza me bada rayuwarta domin lullube Yaranta. In sha Allah ba zan katse maka farincikin ka ba, Allah ya maka albarka ka ya baka me maka biyayya." "Amin Ya Allah, Mother like no other " da haka suka gama waya. Ta kira Fadar sokoto, ta nime ganawa da mai martaba, sun yi magana sosai, da dare da Sultan ya shigo cikin gidan ta, ta kuma isar mishi da bukatar ta akan Sa'ade. "Yanzu ya za ayi?" "Ina son zuwa sokoto naga iyayen yarinyar na nimo mishi aurenta a matsayin Y'a ba surukata ba." "Sauran matan fa?" "Surukaina ne, ita kuma matar auta ce, babu batun surukata ce. Yadda Auta yake shiririntan sa haka itama zan renata da shiririntan." "Kina nufin tura mishi ita zaki yi?" Wani kallo ta masa sannan ta ce mishi. "Saura ka gaya mishi sai na gamu da ku baki ɗaya, ko na fasa nima mishi auren ta." Haka suka yi ta tattaunawa. Kwana biyar a tsakanin Abuturab ya kira ta ya isa london Addu'oin babu wanda bai sha ba, domin idan aka ce maka tana son Abuturab a cikin Yaranta tow bata baki ne, wani irin tausayinsa take ji, haka ta kira Yayunsa Mata suka tattauna sosai, babu wanda ya gaya mishi abin ake shirya mishi, sai da ta cika wata daya, ya kira ta ya ce mata. "Ummina saura wata guda ta gama idda Allah yasa ban takura Miki ba" "Ai kai ko mayye ne sai dai ayi hakuri da kai, ajiye waya" a cikin wata daya da ya rage, hauka ce kawai Abuturab bai yi ba. A kasa da sati Uku Ummi ta fara shirin tawowa sokoto. **** Sokoto. Saura sati ta gama Idda, Abdul sai kai gwauro yake yana kai mari, domin yafi Abuturab shiga tashin hankali, gani yake kowani lokaci zai iya rasa Sa'adatu, a lokacin ne yayi confront din Hajiya Daulah....... *Hahaha next Chapter dole muyi zaɓe a tsakanin iyayen biyu nan* 1=400 2=800 3=1000 08130269641 [04/07, 7:08 pm] usmanlauratu71: Wedding alarm 💐 01... 54.... Izuwa yanzu Abdul yana matukar bata tausayi, gani take bai cancanci wofantarwa haka ba, don haka ta kalle shi cikin tausayi ya ce mishi. "me kake bukata?" "Hajiya me nake bukata bayan kin san abin da nake bukata?" Ya fada a sanyayye. "Sa'ade ko?" Sunkuyar da kai yayi tare da matse hannunsa. "hmm" "Allah yasa iyayenta su baka ita domin ban musu adalci ba." "Hajiya duk wannan me sauki ne, apologies ɗinki suke bukata kina nime su yafe miki zasu yafe miki" shiru tayi kafin ta ce. "Zasu yafe maka kuwa?" "Yes of course tunda ita yarinyar zamu ni ma da Mahaifayar ta " "kana ganin haka yayi maka daidai?" "Eh haka ya min daidai " "yaushe zata gama idda?" "Ina ga nan da two weeks" "ok satin da ta gama idda, sai muje ko?" Ta tambaye shi,.bai so haka ba, amma kuma ya zai yi? Dole ya hakura. "Har yau baka ji labarin Sophia ba ne?" "Wani labarin ta, bayan ta zaɓi aikin ta dani ne zan da ni?" "A'a ba za ayi haka ba" ta fada tana me rarrashin sa. Wasa wasa Hajiya Daula ya sauko ainun domin kuwa kiri-kiri take son farincikinsa da kuma nutsuwarta amma taya zata yi confront din iyayen Sa'ade? Al'amarin ba wasa a cikin sa taya ma zasu kuma bashi auren Yar su, haka dai tayi ta lissafo ranar gama iddar tunda kowa yasan wata uku ne. Sai mace tayi jini uku, idan mai takaba ce zata yi zaman takaba na kwana arba'in, sai idda wata uku, shi zai bada wata hudu da kwana goma, jimulan kwanaki 100 cib, idan kuma macen da tayi mu'amala da maza ce, tana da wata hudu na istibira'i, haka zai bata damar tsarkake mahaifanta daga daukar dattin can, tayi jini hudu. Domin wani lokaci ana samun ciki da zubar jini. Sune hukunce-hukuncen wanka. *** A bangaren Ummi sai da ta ga ya rage kwanaki uku, domin kullum sai Abuturab ya kira ta, ya gaya mata kwanankin da suka rage. Don haka yau tun da ta samu Sultan ta gaya mishi zata Sokoto, ya yarje mata, ta shirya ita da Zakiyyah da Ummy Aymana. Suka bar kwara, karfe biyu na rana suka isa garin Sokoton birnin Shehu, daga gidan sarautar aka zo daukar su a mota, cikin girmamawa. Tun kafin wannan ranar da Sadeeq ya samu labarin zasu zo, da kansa ya tafi har gidan Zakaria ya musu magana yadda zasu fahimce, kuma suka yi maraba da zuwan shi da shawarar da ya kawo musu, shi yasa tun shekaranjiya suka koma Maikulki, ana son a sayiwa Future queen martaba. Musamman garinta da asalinta, sai dai basu gaya musu ranar da zasu zo ba, sai dai Nazif ya zama shi ne jagora akan kome, don haka suna isowa Sadeeq ya gaya mishi shi kuma ya gayawa mahaifinsa. Wani abin dadi da burgewa tun kafin su iso, Mai gari ya saka an gyara bangaren da Aliyu xai zauna a gidansa, aka saka komai dake wancan zuwansa babban Mikano generator aka saka a gidan, amma mai gari ya hana a tadda wai na dan shi ne sai yazo za a kunna ko a tambayi izinin Nazifi. tun kafin su zo an gyara ko ina, harkan gidan Abuturab da ake ginin da ya kai linta kuma alhamdulillahi gida ne na gani a fada, dake dan boko ne gaye nan part daya yayi, shi da matar sa da Future's kids dinsa baya bukatar hayaniya ko tashin hankali. Yana son farincikinsa da na matar sa, baya son cece-ceku. Kuma burin sa a gidan yake son ya kafa tarihi, koda bai kafa ba, yana son Sa'ade ta rayu na wani lokaci a cikin danginta da asalin shi in so samu ne, haihuwar su na farko ya sauka a cikin gidan. Shine dream ɗinsa, shi yasa ake gudanar da ginin a hankali a hankali. Tunda su Inna suka iso mutane sai zuwa suke ana musu barka da dawowa, har da yan tsegumi. Malam Aminu ya shirya cikin shadar shi me kyau, ya nufi gidan Malam Musa kalla. Yadda yaƙe kwad'a sallama zaka rantse da Allah ya shekara bai fansa ba ne. "Ikon Allah ba dai Aminu nake ji ba?" "Yo burinka a daure ni, bai cika ba gani daram na dawo amsar auren Yata a karo na biyu yan gidan mutunci manyan mutane masu mulkin yarbawa." "Ikon Allah ni nake burin a rufe ka?" "Idan ma baka burin dai na dawo hankali zata mutu da haushin salga. Domin Bidiri waadari ya wuceta. " "Allah ya huci zuciyar ka, ba dai don ban xo bane kayi hakuri idan kaji shiri alamar lafiya ce ai" "Hmmm" malam Aminu ya fada, yana yiwa Malam kalla kallon irin baka je birnin ba. "Yanzu ka dawo kenan?" "Eh gamu nan mun dawo ko mu koma ne?" "Kayyasa amma baka da matsala, yanzu me ake ciki?" Gyara zama yayi sannan ya ce mishi. "Yara biyu ne suka taso kaina akan Sa'ade, wannan yaron Bature ashe iyayen sa sarakuna ne,kuma uwarsa zata zo wai ganin Sa'ade. Shi ne aka ce mu dawo gida, me ka gani?" Gyara zama Mallam kalla yayi ya ce mishi. "Kasan dai abin da zan gaya maka, shi ne ka dauki wuka da nama, ka bawa mai gari ba zaka ji kunya ba, ba zamu ji kunya ba, idan har aboki na gari ka ɗauke ni. Tow maza a dauki kome akai gidan mai gari." "Hmm!" "Ka san me yasa nace haka? Saboda a bashi matsayinsa na Uban kasa, haka zai janyo maka daraja sama da shanu dari." "Kai Kalla shanu dari garke guda ne fa " "eh amma ai Sa'ade tafi garke guda ko? Ko kuma zaka kuma sayar da ita ne?" Kunya ce ta lullube shi ya ce mishi."kai dai baka mantuwa wani sayar da ita. Tunda haka kace ba akin ta mutane na yarda da Shawaran ka, Allah ya shige mana gaba." "Yawwa abokina." Haka suka tsayar da magana daya, Washi gari saura kwana biyu, Inna Laminde da kanta ta wanke kan Sa'ade ta kira yar makotar su, ta yarda mata kitso mai kyau siri-siri. Kawai jikinta yana bata wannan karon sa'adenta zata fada hannu na gari, haka suka gama kitson tsaf. da dare Inna Laminde ta mata lalle, hannu da kafa, kar ku ce irin lallen gayu normal lalle ne, irin tsohuwa ta fada kwata, abu biyu ya saka tayi haka, na farko kambun baka, na biyu kambun idanu, tasan idan aka cire rashin magana da rashin jin kunne daya, Sa'ade bata da makusa, mace ce da duk namiji ya gani sai ya ji ta mishi balle kuma irin gwagwarmayar da taci a rayuwar ta, ya saka mata sani akan mutane. Gari na wayewa, hannu da kafarta sun yi jajjajur har wani maroon maroon suke, kafin kace me Inna ta dauko sabon kaya, ta bata. Domin daga gobe iddah ya sauka akanta. Wunin ranar Inna sadaka tayi tayi na shinkafa da wake, sai damammiyar fura da nono wanda ya ji sugar zaii, kafin dare kowa ya shaida Sa'ade gobe zata sauke auren wancan dan banza, Allah ya gani Inna bata kaunar Abdul. Karfe shida ba yamma dab za a shiga sallah magariba Ummi da tawagarta suka isa gidan mai gari, suna parking. Nazifi yana fitowa ya shiga cikin gidan ya wuce dakin injin ya tadda wuta, ko ina na gidan ya wadata da wuta. Yadda mai gari ya ga Ummi ko ba a gaya mishi ba, yaga gyatumar Aliyu, anan ta dauko tsawo da kyan fata irin na shuwa'arab, kyakyawar doguwar mace me sirki da Fulani, shuwa arab, Yarbawa da Hausawa, Yes tana da danganta a kowacce kabila nata ne, shi yasa tafi cancanta zama Sultanah Badi'atul Noor, domin ita kabilu hudu ta haɗa ta fito tsatssonsu. Banbancin ta da sauran matan da suka fito kabilu biyu. "Sannu da zuwa Hajiya, barkan ku da zuwa." "Yawwa Abba da fatan mun same ku lafiya, bari mu shiga daga cikin lokacin sallah yayi." "Madalla barkan ku da zuwa." Haka suka shige cikin gidan. Uwar gidan mai gari da ta Manyan ta, haka ta tarbe su har bangaren abin gwanin dad'i. "Sannu Hajiya zauna ki huta." Kafin kace kwabo an karamma su, Allah da kansa ya ce karraman bani adam, waye ya isa ya wulakanta mutu ai sai jahili, haka kuwa aka yi suna karrama ta, tana musu godiya. Abin ya burge matan mai gari, ashe anan Aliyu ya samu tarbiyya, ashe ba banza ko yaro ne ya mishi aiki zai ce ya gode, girmamawa tana da dadi da burgewa. Kafin kace me gidan ya dauki al'amarin bakin su, daga makota mutane zuwa suke ana kawo abinciin wai ma ba asan yau zasu zo ba, haka aka cika musu gaba da abinci, sallah suka yi tare da cin abinci suka huta, can mai gari ta shigo suka gaisa, sannan ya zauna suka tattauna tare da cewa tazo ganin Sa'ade kawai, tana son ganin yarinyar da ta hana Baba karami ganin kowacce mace da haiba. Dariya aka yi. Mai gari ya ce mata. "Ai kin san yaran mu nan aurar da su muke da wuri, ita daya ce ma ta samu nakasu, amma in sha Allah tana gab da wucewa daga ciki, duk wani cigaba nasan Baba karami zai tsaya mata, soyayyar su gaskiya ce, ba zai yiwu sabida karatu a ajiye shi haka ba, domin ko zama kayi da shi na minti biyar zaka fahimci girman kaunar da yake mata." "Gaskiya ne amma ina ganin a barta ta samu damar kammala karatun mana?" Murmushi yayi irin nasu na manyan, "Hajiya Abuturab yana sonta, kuma zai cika mata mafarkin ta. Amma bana jin sai ta kammala da ace da wani namiji kuka zo sai dai ku tafi da ita domin ko ni zan bashi auren ta." "Murmushin jin dadi tayi sannan ta ce. "Shi kenan Allah ya basu zaman lafiya, saka ranar sai mu sake shiri." "Hajiya kenan ki nime izinin daga mai martaba a daura auren kun dawo daukar ta, domin samun irin Aliyu a rayuwar Sa'addah sa'a ce, tun tana yar ficiciya yake dawainiya da ita, yau sai a ce za a ja mishi rai. Allah kai mu gobe." Wani irin abu Ummi ta ji ya cika mata kai, wayyo Baba karami me yayiwa mutnen garin nan,a daren ta kira Sultan Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari ta gaya mishi. Murmushi yayi ya ce mata, ta bawa Mai gari, babu shiri kuwa ta saka aka kira shi,aka bashi wayar suka yi magana irinta mazan jiya, aka kuma tsayar da ranar juma'a wannan makon za ayi kome, don haka jibi su gobe su Ummi su koma ayi kyakyawan shiri. Ummi tasan dole tafiyar safiya zasu yi don haka, ta mike. "Kun san Allah ku tashi na je naga dota " "ok Ummi domin gobe da wuri zamu wuce sai mun ga ginin shi ko?" "Eh Addah" inji Ummyn Aymana. Baki daya suka wuce gidan su Sa'ade, suna zaune a tsakar gida, tana duba wani littafin su na boko don bakin naci ta haddace littafin baki dayansa. Shigowar Nazifi yasa ta fadada fara'arta, tana sanye da riga da sani, sun zauna daram a jikinta, kugun nan ya fito cass. Tudun Wada shima ya gyara ta. Duk da hasken Fitilar kwan da aka saka sai da Ummi tayi ya tasbihi, wallahi ba zata bawa Aliyu yar karamar damar da zai hana yar mutane sakat ba. Gwanin ban sha'awa. "Sannunnku Nazifi kai ne da kanka." "Eh wallahi Inna na kawo Ummin Yallabai Aliyu ne, gasu nan" "Barka da zuwa sannunku bayin Allah kuyi hakuri ko ina dubu. Larai ga baki fa." Ta fito tana faɗin. "Sannun ku da zuwa." "Yawwa ba zuwan ku nayi ba, Innar Sa'ade nazo ganin Sa'adatun da ta hana Abuturab hutawa ne, ashha ashe yaron nan bakin sa ya boye abubuwa dayawa Masha Allah,Inna ni ba suruka zaku bani ba, Y'a zaku bani." "Yo Hajiya ina matsayin Uban ango sai kin nemi izinin wallahi ko yanzu dauke ta ku tafi ai Aliyu yaron kirki ne." "Ayi haka? Ni dai na bar muku shi ku bani Y'a zaku bani ba suruka ba." Inda Sa'ade take Inna Larai ta nufa, ta riko hannun ta, ta kawo ta har gaban Ummin. "Ga Yarki nan, halak malak mun baki ita ko akwai wani abu da kike bukata!" Kura mata idanu yayi Mansurah ce take yawa a fuskar Sa'ade, tabbas kome yana jiran lokaci mutuwar wani tashin wani. Cikin muryan kuka tace . "Na gode" ta fara tambayarta da Yaren Kurame, "kina son shi?" Boye fuskar ta tayi, tare da gyada kai ko bata san meye so ba, Aliyu special ne a wurinta, how comes zata yi rejected ɗinsa, bayan shi yace ta jira. "Da ni da shi waye kika fi so?" Hade hannunta tayi, dunkulen hannun ta, tayi ya saka a Kirjinta, sannan ya sunkuyar da kai, tare da rike wuyarta. Wato na rantse da Allah ina son ku sama da kaina. Wani irin blush Ummi take tana kara jin kaunar Sa'ade no wonder Aliyu ya haukace, wani irin shiga rai take da shi a zama daya. "Aigooo! Ummi tunda kika samu In-law kin manta da mu." "Na gaya muku ba In-law bace Y'ata ce... (🧟 Ba zaku bar ni na huta ba 😭🚶🏽‍♀️🚶🙄😬😪) Mai_Dambu [06/07, 8:53 am] usmanlauratu71: The wedding day. 56.... Allah bai tab'a kuskuren halitta ba, tun daga mutanen farko har na karshe har zuwa tashin alkiyama. Duk wani halittar da Allah yayi mai kyau ne, haka yasa yayi wasu mabanbanta daga wasun su,.a yau Asabar daukacin al'ummar garin Maikulki suka shaida daurin auren Aliyu Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari tare da Sa'adatu Aminu Fulani, akan sisin gwal na nera miliyan biyu, wanda kowa yasan al'adar shuwa arab ce, a cikin yan zuwa daukar amarya aka kawo wasu manyan manyan awarwaro munduwarsu har guda shida, tare da sarkan kafa da zoben su. Sai wata Sudan lafayya me matukar kyau da tsada, aka ajiyewa Inna. "Wannan sakon daga fadar shehuri ne, domin kawata matar jikar shi, hajjja Nana ta turo mata." Fito da sa'ade aka yi wacce take sanye da Super exclusive, aka shiga daura mata hawaye na zuba mata, sai kallon yayunta mata take, kafin kace kwabo an shirya ta cikin shigar alfarma, kasancewar an zuba mata uban dukiya a jiki yasa aka watsa jami'an tsaro kaca-kace, gidan Abuturab da aka gama anan aka wuce da ita kafin a gama shirin nufar birnin Shehu. A bangaren Inna Laminde kamar bata taɓa aurar da Y'a ba, domin a cikin sati biyu da aka saka tayi bajintar da ko shi malam Aminu bai yi ba, bikin yar gata da dan gata, a matan Sultan an tawo da hajiya Turai da Mariyah sai a can ya rage Ummi da Badariyyah. Wani abin burgewa so suke su ga Sa'ade su samu na gulma, amma Ummi da ta wakilta Rumaisah ta ce kar ta sake a ganta, ta kawo mata yarta lafiya lau. Haka aka yi ta hidima, har rana tayi aka ɗauki amarya, aka kai ta gidan mai gari, daga nan aka wuce da ita sokoto. Sai a lokacin tayi ta kuka, da yar karamar borinta ita babu inda zata ta bar Innarta, ita kanta Inna shi yasa taki yarda su hadu tun da aka daura aure aka fita da ita zuwa gidan Abuturab ta sakawa zuciyarta sallama, da Rumaisah zata fita da ita ne ma ta ce mata. "Idan kin je kice mishi don Allah kukan da tayi ya isa haka, ya taimaka min kar tayi kuka domin zan ji babu dad'i." "In sha Allah Innar mu ba zata kuma kuka ba, domin ta gama shi kenan har abada." Haka aka tafi da ita, da farko Sa'ade ta zata za'a dawo da ita wurin Inna ce sai ta ga babu zancen haka. Karfe biyar na yamma suka isa sokoto, ashe dayawan yan daurin auren sun tafi ma, domin ana daura aure sha daya suka dawo sokoto, sannan suka yi liyafa, kafin suka wuce dake kusan harkar jirgi ne, anyi jigila da su, kuma idan da mota ce sai an kwashi kwana uku ana abu daya, dake an mata jere a can Maikulki kamar yadda Ummi tace ita kawai ake bukata, basu bata lokaci ba, aka wuce da ita airport. Koda suka isa kamar an san da zuwan su, domin kome an shirya, bayan an dibe su. Sai lokacin Rumaisah ta sauke ajiyar zuciya, domin alkawarin Ummi ta dauka, na cewa tabbatar da ta kawo mata Yarta gida, koda suka bar sokoto. Bakwai na dare suka isa yadda zaka fahimci auren yan gata ne, domin tun daga airport har gida jami'an tsaro ne, koda suka isa sun gaji libis, ita kan Sa'ade sallah tayi ta kwanta, saboda gajiya ko a ina suka samu hotunan da suka yi calander, memo, stickers na hotonsu. A daya daga cikin hoton ma check ne a jikinta, na makaranta wanda suke sakawa ranar visiting. Haka aka yi ya hidima, washi gari babu ango amma fa an yi gagarumin bukin na fada a ji, domin duk cikin Yaranta babu wanda aka yiwa irin wannan bikin sai auta mowan Y'aya, kuma kowa yazo bikin sai da ya tafi da garan biki. Kwana biyu aka yi ana biki, kafin aka watse, yan uwan Sa'ade sun san ayi aurenta gidan da ake bukatar ta, domin har babban falon Sultan aka kai su, har da ita Sa'aden, cikin jin dadi da farincikin yake kallon Sa'ade, lallai baba karami zai more rayuwar shi, domin yarinya ce karama wacce zai daurata a duk inda ya mishi. Addu'a sosai yayi musu sannan suka bar part dinsa, washi gari suka tashi da niyyar Komawa gida, anan aka ga tashin hankali. Kuka take tana rike Rabi, dakyar aka rabasu Ummi ta riko ta har ɗakinta na sama, ta kaita domin bata bari an kaita part din Abuturab da yake cikin gidan ba, rarrashinta take dakyar tayi shiru. After few days kome ya lafa,.an samu natsuwa takanas aka kawo me gyaran jikin Amar'e daga Chad, aka fara gyara Amarya. Lekowa dakin Ummi tayi ta same ta, ana turara mata gashin kanta. "Yawwa don Allah kamshin ya zauna a jikinta na few weeks, ina son ko zama tayi, ta bar wurin a san ta zauna. " "Inshallah." Murmushi kawai Ummi tayi ta mika mata bowl din fruit da aka yi blende din shi aka zuba zuma da madara, ta karba tana me sunkuyar da kanta, domin jikinta ba wani kaya ba ne a jikin armless ne mara nauyi wanda zata ji dadin sakewa a cikin sa. Haka ana cigaba da kulawa da jikin ta, sai da suka dauki kwanaki goma ana turara gashinta kafin aka dawo jikinta baki daya. Sosai ake kulawa da cimmar ta, abin shanta. Hatta inda zata zauna. *** Abdul Wato idan Ubangiji ya shirya nashi al'amarin ko babu wanda ya isa fahimtar kome akai, da wannan yanayin Abdul da uwar shi suke ta shirya yadda zasu fuskanci iyayen Sa'ade, kwana goma sha biyar da daura auren Sa'ade kuwa suka dira a garin Maikulki, shi kan Dr Sharif yasan abin da ya faru babu amfanin yayi musu bayani tunda ya tattara uwa da d'a, ua zuba musu na mujiya. Yasan an yi auren Abuturab da Sa'ade. Don haka suka shirya shatara na arzikn saka kaiwa iyayen Sa'ade kwadayayyun mayyu masu shegen son abun duniya ba. Koda suka isa gidan Abdul ya sha mamaki ganin yadda kome ya sauya, da sallama suka shiga cikin gidan. "Lale maraba da zuwan ku, lallai gidan da manyan baki ne" inji Inna Larai, d'aga labulen Inna Laminde tayi suka yi ta sakar musu murmushi ta fito tana faɗin. "sannu ku da zuwa maraba lale," ta fito suka gaisa. "Inna mun same mu lafiya?" " Alhamdulillahi, ya kwana biyu." "Masha Allah, sai godiya." Ita kan Hajiya Daulah bata iya cewa kome ba, "sannun ku da zuwa. Da fatan dai lafiya ya kawo ku?" "Lafiyar kenan." Hajiya Daulah ta faɗa, gyara zama suka yi sannan suka koro jawabi. Murmushi Inna tayi sannan ta ce musu. "Ikon Allah, na zaune ya fadi kun zata Sa'aden yar tsana ce da zan ajiye ta har yanzu? Tab tow ai kuwa yau satinta biyu a dakin mijinta, ba ma haka ba, ai ko a duniyar mafarki bana fatan sa'ade ta koma rayuwar ka, balle a duniyar ido biyu. Ba zan rantse ba, amma kuma nasan tayi nisan da ba zata tab'a dawowa kasa nan kusa ba, domin Aliyu ba irin Mazan nan bane da zai sake ta, tayi wasararai bai san darajar ta ba. Rabuwar ku, ka saka a ranka har abada kamar baku tab'a zama ba.". "A'a Innar Sa'adatu ki taimaka a dawo mishi matarsa." " Ta ina ta zama matarsa?" Inna ta tambaye ta,tana murmushi. " A dai duba al'amarin tunda suna son juna " "waye ya gaya miki tana son shi, Uwar Aliyu tazo nan ta nemi ba bata Y'a ba suruka ba, sai dan nafi kowa rashin zuciya na ce a'a bayan ita yar ba baiwa va ce, ki ji da kyau Sa'ade na, ta tafi kenan " "wallahi Inna ina son matata." Murmushi tayi mishi ta ce mishi."Sau daya ake samun dama. Idan ta subuce maka ta subuce kenan!" Kamar ba namiji ba, Abdul yayi ta kuka yana rokon a dawo mishi da matarsa. Amma ina haka suka gama haukarsu suka mike zasu tafi. "Innar Sa'ade da kinsan wacece ni ba zaku tab'a gaya mana cewa mun tasa sa'ade ba, Allah na tuba meye kudi baya badawa. Kuma da karfin tsiya zan dawo mishi da matarsa." Murmushi Inna tayi ta ce mata. "Allah ya baku Sa'a kuje tana auren ɗan Sarkin Kwara, ba mamaki su baku ita idan basu baku ba, Hajiya Badi'atul ta gaya miki abin da ya dace." Haka suka bar garin Abdul yana kukan ya rasa mintin zuciyar shi. Wasa wasa suka kulla lallai sai sun tafi kwara. *** A can sati Uku aka gama gyaran jikin Sa'ade, ga Abuturab ya dame ta da lallai a kawo Sa'ade a mata aiki ta ce mishi ita zata kawo a mata aikin,. Bayan tafiyar me gyaran jikin ne, aka shirya musu tafiya a yammacin Laraba, suka nufi lagos a can jirginsu ya tashi zuwa Birtaniya. --- sun isa a wayewar Alhamis. Suka isa gashi garin ana mugun sanyi, tun a addis Ababa suka sayi kayan sanyi sosai domin sanyin ya fara a wurin, kuma nan da wasu kwanaki zai zama da dusar ƙanƙara. Kurawa Ummi yayi yaga babu alamar Sa'aden, jikin shi a mace ya matsa kusa da ita. "Barka da hanya." "Yawwa baba karami." Ta fada tana kallon shi, ganin yadda fuskar shi ya nuna rashin jin dadin sa, yasa ta matsawa kaɗan. Idanun shi ta sauka akanta, ta sha zanen lalle jajjur da ratsin baki, "Just for you dukka taka ce." Kasa magana yayi, ya kalli hagu ya kalli dama, sannan ya ce mata. "Ummina Are You kidding me?" "Ni kakar ce" kafin ta gama rufe baki, ya juya ya kalli Gabas yayi sujadul shukuryya, kafin ya mike ya rungume Umminsa, yana me riko hannun Sa'aden. "sake ni ka rike matar ka!" A hankali ya sake Ummi sannan ya janyota, tare da juyata yana me rungume ta bayanta, saka hannu yayi ya runkukkuneta. Yana jin kamar ya dauke ta. "Thank you Ummina." Bai san ina zai saka mata biyun nan ba, yana son Ummi domin ita ce First love dinsa, ita ta kawo shi wannan duniyar ta cancanci kauna na musamman. Ita kuma Sa'ade kaunar rayuwar shi ce. "sake min Ya mara kunya sai rungume ta kake?" D'ago kai yayi cike da kauna yana kallon Umminsa ya kasa magana sai murmushi, daga idanun shi zaka hango zallar kauna ce mara algus. Dakyar ya sake ta suka nufi gidan. Ummi tana gefen shi, Sa'ade tana baya, sai kallonta yake a madubi. "Baba karami nan garin ba naija ba ne don Allah kar ka watsa mu a titi." Murmushi yayi har suka isa, ya kasa boye farincikin sa, amma babu irin azazzben rawan kan nan, sai dai daga yanayin da zaka fahimci yana cikin mugun farinciki, dakyar ya iya hakuri tare da barinta da Ummin ba wai ko wani abu yake bukata ba, a'a'kawai irin.farincikin nan ne na abinda kake mugun so amma baka da saka rai kansa, ya zo maka ba zata. Haka yake jin kamar an saka wing ya tashi sama, yana he can fly away, kamar dai irin tsuntsu me yanci zai iya zaga ko ina, tabbas ba zai je mata a matsayin miji ba, dole ya koya mata kwarkwar da yadda zata hau bishiyar kace akansa. Yadda da iya idanu zata fahimci ya dace da ita, yake ta shirya yadda zai zauna da ita. Ga wani abu da yake sosa mishi zuciya yana jin wani irin kaikayi. Kamar zai dauke ta ya zura da gudu. Sai dare ya sake samun ganin su. Domin an tattauna da muhawara mai zafi, domin akan al'amarin Latifa da Abuturab ne, yadda Ummi tayiwa Baban Mansurah bayani ya fahimta, kuma ya gane hakan tuntuni domin yar ta gaya Mishi gaskiya. Don haka aka saka Abuturab a gaba ya sawwake mata, kallon ta Ummi tayi ta ce mata. "Kin san abubuwa dayawa, a cikin shi kuwa har da sanadin mutuwar Maina da Mansurah bani files tare da min bayanin waye yake da hannu a cikin kawowa Sa'adatu hari a park." A razane Latifah ta ja da baya..... (Wash..... Mission impossible) #Mai_Dambu [06/07, 6:14 pm] usmanlauratu71: 57.... "Kenan ta san wani abu akan mutuwar Maina?" Hàdiye yawun bakinta tai, tare da ja da baya. Sakamakon jin tambayar Babanta ya wurga mata, "Wallahi ban san kome ba, na rantse da Allah." Kura mata idanu Ummi tayi sannan ta ce mata. "Ba zan miki dole ki fadi gaskiya ba, sai dai adalci daya zan miki shi ne zan raba ki da Aliyou domin macen da tasan darajar rayuwa ta dace da shi, sannan ku shaida ba zan kuma ce mata ta gaya min gaskiyar me ta sani akan Maina ba, amma zan barta da Faduwar rana da fitowarsa, har yau na kasa nutsuwa akan mutuwar su, amma zan bar ki da Allah domin ke tawa ce haka ba yana nufin zan iya daukar abin da kike da masaniya akai ba. Yaya Khamal ka zama shaida" "Latifah me kike sani akan mutuwar Maina?" "Wallahi ban san kome ba!" "Baki san kome ba?" Bayan Mamanta ta tambaye ta, murmushi Hajiya Kudirat tayi sannan ta ce mata. "Tunda baki san kome ba meye na shiga damuwa da firgici? Amma Badi'atul kiyi hakuri a cigaba da bincike, kuma ina tare da ke ko nice ba zan iya barin dana ya zauna da ita ba, bayan tasan kome akan mutuwar Maina!" "Ba damuwa Kudirat Allah ya sa mu dace." Kallon Aliyou Ummi tai tasan kwanan zancen. "Baba karami baka ga dare yayi ba ne?" Ware idanu yayi tare da tab'e baki, ya ce mata. "Ummina na zo miki sai da safe ne." "Toh Allah ya tashe mu lafiya " dariya Maman Latifa ta musu. "kin rike mishi mata kice ya tafi ya kwanta, ai baki so gaskiya ba." "Ta gaji ne" ta fada tana dauke kanta, Mikewa yayi ya nufi hanyar dakin da Ummin ta sauka, ya same ta kwance cikin bargo, tayi lumo ga room heater, a hankali ya isa har bakin gadon ya zauna tare da kunna wutar bakin gadon idanunta tar cikin na shi. Riko hannunta yayi yana murzawa a hankali. Kafin ya sumbaci hannun yana kallon yadda ta lumshe idanunta. Sannu sannu ya cigaba da murza hannun har ya ga ta fara hamma, yana hango yadda ya kashe mata jiki da mata tausa, wasa wasa har barci yayi gaba da ita, ya ja bargon ya rufe ta. Sannan ya fito. "Kaniyarka ka zauna yin a dakin?" "Ummi kawai ki biya ni ladan reno." "Hmm." "Allah ya shirya ka" ya fita yana dariya, domin wani irin nishadi yake ji. Haka suka watse, babu yadda iyayen Latifah basu yi da ita ta gaya musu gaskiya ba, amma yar mai taurin kan tsiya taki magana, dole Ummi ta saka Aliyou ya sake ta, kuma a gaban su ya ce dama babu iddarsa akanta, ba zaka iya gane fushinta ko fahimtar yadda take ji da sake ta da Aliyu yayi ba, amma tabbas tana wani irin konewa ne ta cikinta, wanda take kuka a boye. *** A can Sokoto kuwa kwana biyu da barinsu Maikulki, suka hada hujjojin bogi suka nufi kwara. Dama an ce mara kunya duk inda yake sai ya nuna halin sa, haka ce ta faru domin kwanan su daya da isa kwara, suka nufi masarautar, daga yanayin yadda ake karɓe su, jikin Abdul yayi la'asar. Ashe karyan arzikn uwarsa take, domin duk wani abu na cigaba akwai shi a cikin masarautar, da aka kai su mansion din Sultanate sai suka sake baki, domin dai Hajiya Daulah duk wankata ba zata iya saka diamond haka tana hutawa da shi, sannan ga maid ta ko ina sai aikin kaiwa da komowa suke, tana zaune Sultanate ta fito rike da sanda. Kallon juna suka yi kafin suka mike tsaye, har ta zauna domin sun samu falon da Hajiya Suhailah. Ganin Sultanate yasa ta mikewa sai da ta zauna duk suka zauna. "Barka da warhaka Sultanate, ga baki daga sokoto nan, zan je na dawo." "Zauna domin naga bakin babu alkhairi a tattare da su." Ta fada tana kallon Hajiya Daulah. "Ina jinki" ta fada tana me kallon Abdul. "Hajiya suna na Daulah!" A dan razane suka kalli juna, kafin ta ce mata. " Hmm ina jinki" gyara zama tayi sannan ta fara bata labarin abin da ya faru. "Wannan yarona ne, Abdulhakim Abuturab ya turawa iyayen matarsa kudi suka kashe auren bayan har da cikin shi suka zubar mishi da shi, anyi adalci anan? Hajiya mun zo nan ne domin jin cewa kina da kokarin kamanta adalci, da naso na maka Aliyu a kotu da uwar su." Kwarewa Hajiya Suhailah tayi da ruwan da take sha, idanunta suka yi jajjur. " Sannu kin kware ne?" Sultanate ta tambaye ta. "Eh amma ba ruwan ne ya kwarar dani ba, jin cinnaka zata yi fada da giwa ne!" Ta fada tana dariya. "Hajiya kin san wace ce ni kuwa?" "Hala baki san wace ce Badi'atul Noor ba ko? Da tana nan ke da kanki zaki gane kuskuren ki ba kwaso rigima da ita. Bari na gaya miki ke daya baki isa ki kawo hujjar da zaki kalubalance ta ba, amma ga Sultanate nan" ya fada tana dariya. "Ita wacece a gidan nan?" "Surukata ce, da bata dauke ni da daraja ba, da nasan bazawara ta aurawa jikana sai na hana auren yanzu ma bata b'aci ba, bari ka kira shi sakaran da ya daure mata gindin Iskanci a gidan nan." Yadda Abdul ya marairaice zaka rantse da Allah zalintar shi aka yi, nan kuwa dan banza sharrin su ya kawo su. Haka aka kira Sultan babu shiri ya shigo mansion din, aka gaya masa kome. Kallon Hajiya Daulah yayi sannan ya kalli Abdulhakim. "Kuyi hakuri da abin da zan faɗa muku hala ba zai muku dadi ba, Baba karami bai auri matar ka ba, asalima akan kunne na aka yi shara'arku a fadar sokoto anyi haka ko ba ayi ba?" Ya zubawa Abdul idanu, jikin shi yana rawa ya ce mishi. "Eh Allah ya baka nasara, kar ka manta nima da ne, idan aka raba ni da Za'a ba a min adalci ba, ya sake min mata ta don Allah." Ya fada yana kuka. Murmusawa Mai Martaba yayi ya ce mishi. "Ba ni na nima mishi auren ba, uwarsa ce bani da zarafin da xan ce yayi abu tunda yana da hakkin uwa akansa, ita ta fini sanin ciwon shi da zafinsa, don haka zan kira ta ayi magana da ita. " "Kenan Abdulrahman ba zaka iya sakawa Aliyu ya sake mishi matar shi ba? Bazawara ce fa? Sai kace kana tsoron Badi'atul Noor ɗin!" "A'a Umma kowa da matsayinsa, da kika ce ba zan zauna da iya ita ba, ban miki biyayya na auri irin matan da kike so ba? Shima kuwa kin ga ba zan tauye shi ya yi abin da nake so ba, yayiwa mahaifiyar shi biyayya nima na miki, wannan shi ne adalci a tsakanin mu." Shiru Hajiya Daulah tayi tana mamakin tsage gaskiyar Sultan idan shi ya kasance me tsage gaskiyar haka ya Matar shi zata kasance. Kiran wayarta da yaje yi ne ya shiga, a hankali ya fara bayani. Shiru aka yi kafin Abuturab ya ce mishi. "Abba Ummina tana sallah ne, bari ta gama sai na kira ka, Abba!!!" "Na'am Aliyu" "Abba wallahi idan Abdul bai daina bibiyarta ba idan na kama shi sai na kashe shi har lahira, ya fita harkokin mata ta." "Ubana kishi ko? Kar ka damu kayi tattalin matarka yadda babu me iya hangonta a cikin gidanka." Shi kenan Abudul ya fada domin maganar kamar a fili suke, bayan sun gama wayar ya kalli Sultanate ya ce mata. "Umma Badi'atul tana sallah " "idan taso tayi gware da bango karewar sallah, ina jiran ta." "Hajiya mutuwa zanyi idan na rasa Sa'ade" sai kuka yake sharba, shi ma kuma Sultan gefe daya baya fatar rana masoya biyun nan haka kawai, a saka mishi da ya sake yarinyar da yasan ko mata nawa Baba karami zai aura ba zai samu kamar ta ba? Don haka karya ne babu me sakawa ya sake Sa'ade wallahi. Bayan kamar minti Talatin, Ummi ta kira suka fara waya, babu hayaniya Ummi ta ce mata. "Kika ce matar sa ce da ciki?" "Eh mana." "Ok sati na sama zan zo, amma ki sani ba zan tab'a sakawa Aliyu ya sake sa'ade ba, duk abin da zaku yi kuyi sannan zan zo da nawa shaidar cewa bata dauki cikin sa ba." "Hajiya kar ki nuna min karfin mulki ina da dukiyar da zan iya ja da kowa!" "Ai dama ba dukiya zan gwada miki,, idanuna nake son ji gani sai ki maimaita abin da kika fada." "Har ke wace ce da zaki ce zan maimaita!" "Nice Badi'atul Noor, wacce tayi Imani da Allah sa ƙaddara, wacce take raba dare da rana domin yaranta, da na al'umma baki ɗaya. " "Wallahi ki tabbatar kin dawo min da Surukata." "Tab sai dai nazo din, amma bana fatan haka, domin gara naga gawar sa'ade da akan na baku ita kinji ai domin ni Y'a na auro mishi ba suruka ba, nan gaba kuwa su haifa min jikar fari na goya abina " daga haka ta kashe wayar, yayin da Hajiya Daula ta bar falon a fusace. Ita fa wannan matar dauka take Badi'atul Noor kanwar lasa ce. Haka aka yi ta kacan-kacanna maganar kamar me, ya zama babban magana a cikin masarautar. *** UK. Idanun shine akan Sa'ade da ta tsuguna gaban wani kare, gwanin ban sha'awa fari tass. Kamar ta dauke ta gudu. "Ummina!" Ta fahimci akwai abubuwan da yake son fada da kuma wanda yake damun sa. "Kar ka damu da abin da yake faru." "Ummi kina ganin lucky har zata iya daukar cikin sa?" Murmushi tayi tana gutsiran Peach, "karya ne Lucky bata dauki cikinsa ba, kawai yana son ya raba ku ne" "Ummina tow me yasa yake bibiyar ta " kurawa yarinyar idanu tayi ganin yadda take tsalle-tsalle da karen yasa ta cewa. "Saboda babu abin da ya tab'a shiga tsakanin su na aure, ga koshi ga kwanar yunwa. Bai taba zaton zaka aure ta a bazawara ba, bayan kasan ya ce kun zubar mata da ciki, yanzu haka sabon rigimar shi ne Sultanate ba zata yarda da maganar auren ku ba, zata ce ka auri Budurwa a cikin familyn ta, domin a tabbatar gaba ka zama next King.......(🙄😬😂🤣) #Mai_Dambu [07/07, 8:22 am] usmanlauratu71: 58...... Ware idanu yayi kafin ya ce mata,"Ni din za ayiwa auren dole?" Murmusawa Ummi tayi tana faɗin. "Kai mana." Bata rai yayi ya ce mata. "Don Allah kiyi wani abu ni fa, Lucky nake so " murmushi tayi sannan ta ce masa."aikin ta zai dauki wata nawa?" "Wata uku!" Ya bata amsa, kallon Sa'ade tayi da take tsaye da masu karen dama ya fito ba a sani ba ne, daukar karen suka yi suna mata godiya, itama tana musu magana da hannu, haka suka juya suka fita, ta dawo wurin su Ummi ta zauna tana me tagumi. "Zaka iya hakuri da ita?" Ware idanu yayi yana kallon kasa, domin ya fahimci inda Umminsa ta dosa. "Duk yadda kika ce!" "Alhamdulillahi, ka rike ta da amana, indai yadda nake hasashe ne tabbas dole Abdul da Uwarsa su bukaci a sake musu ita, kai ɗaya ne zaka iya maganin wannan al'amarin tunda sun samu Sultanate, kuma ina son na hana kowa iko akan ka, dole duk wani abin da zai faru ya faru a cikin gidan, be a good Man, ka tsaya domin kare matar ka, idan har kayi hakuri na wasu lokutan ina son na kara baka hakuri akan na yau" murmusawa yayi a ransa yana faɗin. *Ummina ai ko baki fada ba, lucky ba irin wacce zan mata gaggawa ba ne, bana cikin maza musu kwadayi da zallama.* Sannan aikin da za a mata, yana bukatar nutsuwa da kwanciyar hankali, shi yasa zai d'aga mata kafa, za ayi aikin wata uku kuma sau biyu ne ko sau uku. Haka yasa shi dole zai d'aga mata kafa, ya ce mata. "Ummi aikinta yana bukatar kwanciyar hankali, baya bukatar hayaniya ko takuri." "Allah ya dafa muku." "Amin Ya Allah." Ya furta, tashi Ummi tayi tana faɗin. "Ina son na sauya mata kayan gidan kafin na wuce ya zamu yi?" Gyara zama yayi yana faɗin. "Da a bar wannan din tunda nima na kusan gama karatuna, idan na gama zan dawo ne baki daya. Ni da london sai hutu ko kawo lucky ganin likita" murmushi tayi sannan ta ce. "Kana nufin zaka dawo bayan an gama mata aikin?" "Eh Ummina na kusan kammala project dina nan da wata huɗu, shi yasa kawai gara na dawo gida gudu ya kare, na samu macen da nake so, ina son zama cikin dangina da mahaifana." "Baba ya girma kan, zai dawo ya tallafe ni " "in sha Allah, Ummina." Ya fada yana riko hannun Sa'ade, "Ummi bani aron ta, mu shiga gari!" "Almuru tayi fa" "ai daidai kenan" ya janyo hannunta, suka wuce. "Allah ka dawwamar da soyayyar su har abada, Ya Allah ka kare su daga sharrin abokan halitta, Ya Allah ka shiga tsakanin su daga sharrin masu kulle-kulle, ya Allah ka albarkace su da zuri'a dayyiba nafi'ann." Tana gama addu'ar ta nufi cikin gidan, tana jin wani irin nutsuwa a ranta. Shi kuwa Abuturab yana daukarta asibiti suka nufa, sai da suka ga likitan da ya fara duba ta, kafin aka kuma bata magani na kwana uku, domin a kara fahimtar inda ciwon yake, daga nan asibitin gidan wani abokinsa da yake unguwar ya kaita, tare da gabatar musu ita, abokin shima dan Nijeriya ne, anan suka yi sallah magriba da isha, matar me suna Faleesah matar da mijin yan azare ne, na garin Bauchi. Anan suka sha hira, da zasu tafi Faleesah ta dauki kayan gyaran jiki ta bata, har da rubuta mata, amfaninsu, haka suka tawo sai godiya suke. Lokacin da suka iso gida abin ka da mara wayo daukar kayan tayi ta mikawa Ummi, tana gaya mata ai matar abokinsa ce ta bata dukkan kayan. A daki Ummi ta bude kayan, kallon Sa'ade tayi da ta shige ban daki abin ta, murmushi tayi me hade da dariya. "Kuruci dangin hauka, a bata magani ta kawo min, wannan yanayin naki Y'ata zaki ji jiki a hannun baban karami" haka ta ajiye kayan washi gari, ta saka ta a gaba har zuwa part din Abuturab din, ta shirya mata kayanta. Sannan itama tazo mata da kayanta. zuba mata ba a firij ta kirata, a nutse take mata bayani, tare da gaya mata ta sha maganin, domin ya zauna a jikinta. Musamman irin su Honeydrop, na mss Flowers, gumba da zumar Maman zeey da Dambu. Tunda ta bata kaɗan taci, a take Sa'ade ta gama rayawa a ranta, duk sai ta kuma sha, kuma abin da Ummi ta ce mata tana shan rabin kofi, amma yar yar nan cewa take ita kofi guda zai isheta, dambun kuwa tunda Ya nama ce, cin dare daya zata masa ya ƙare, kayyasa. Haka Ummi ta jata har kitchen ta nuna mata kome, muryansa ummi ta ji yana faɗin. "Ai ni mata ta, ba zata shiga kitchen ba, ina aiki a gidan abinci ai dole na koya, don haka kyaleta ta huta abinta. Idan muka dawo naija kin koya mata" "Baba karami me yasa baka kunya ta?" "Kai Ummina wani kunya dai? Tow shi kenan na fara jin kunyar ki daga yau." Ya rufe fuskar shi. "Ina son komawa ne yau, shi yasa na kawo maka ita, Baba karami ga amanar yar mutane, don Allah ka rufa min asiri ka zauna da ita lafiya, baba karami na san halin ka, na san waye kai kayi hakuri da halinta, ka san ba isasshen lafiya ce da ita ba, don Allah a kula da rayuwarta. Kamar kanwa ce maka, dan ne ma da a garin su ce ma, hala ka haifi sa'anta, don Allah ka rike ta da amana." Tura baki yayi yana faɗin. "Kin bani amanarta, ni kuma waye zai rike ni?" "Allah zai rike ka, in sha Allah ba zaka ji kunyar duniya da lahira ba, addu'a ta ba zata fadi banza ba, domin kullum ina rokon Allah akan ku baki daya" "Ummina na gode Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana " "Amin Ya Allah " sannan ya riko hannunta ta daurra akan na Abuturab. "Banda rashin ji, ban da rashin kunya nasan ba halin ki ba ne, ki kula da kanki da shi, idan ya miki laifi ki turo min sako, zan zo na zane miki shi ." Murmusawa tayi tana boye fuskartar a gefen kafad'ar shi, "Ummina kar ki saka ta rena ni, domin ba yarda zan yi ba." "Murmushi tayi sannan ta ce. "na barku cikin amincin Allah" daga haka ta tafi, ganin zata bita ya riko hannunta, tare da zuba mata wasu narkankkun kallo, kamar wacce aka makewa gwiwa ta koma gefen kafad'ar shi ta tsaya. Janyota yayi gaban shi, ya tallafi fuskar ta yana me goga mata hancinsa. Dake akwai Yaranta a kanta janye fuskar ta, tayi tana me nuna mishi cikin firji. Ummi ta saka mata kayan dad'i. Ware idanu yayi yana tambayar ta. "really?" Gyada masa kai tayi, a hankali ya jata zuwa firji din, budewa tayi ta fara janyo jarkar zuma, bai tab'a gani ba kuma bai san me ake dasu ba, don haka yaga ta dibo a kofi ta mika mishi. Amsa yayi ya kai hancinsa, kamshin kanumfari yasa shi kallonta ta. Da idanu ya tambaye ta. "duk na wa ne?" Gyada masa kai tayi, kambu ai kuwa ya sha har yana niman kari, itama ta diba tana sha, tare da ciro mishi gumba, tana ci yana ci. (😂🤣 Kankantaran uba zaku gayawa mutanen garin london) haka suka ci sosai har dambun namar, abin dariya sai da ya dauke ta a gaban firji din domin baki daya, so take ta cinye ta huta da dadin da take ji. Haka suka sha hiran su, sannan ya nuna mata dakin da zata kwana domin idan ta gama shan magani zata koma asibiti har sai an gama aikin. Aikuwa kowa ya kama gabansa ya nufi dakin ya kwanta. Shi kan tun a wurin wanka ya fara gano lafiyar sa tana bukatar a gaji, sai ya dauka ko dan hiran da yayi da ita ne, haka dakyar ya gama wanka. Nan jikinsa ya dauki dumi, abu fa yaki yarda a zauna lafiya. Wucewa kitchen yayi ya tafasa ruwan zafi, ya zuba gishiri da lemon tsami, ya sha sosai a hankali ya ji maran da tana sakewa, kafin daga bisa ni ya wuce dakinsa, yasan za ayi haka. Duk yadda aka yi a cikin abin da suka ce ne. Shi yasa koda ya kwanta dakyar yayi barci rub da ciki, domin shi daya yasan yadda yake ji. Ita kan Hajiya babu abin da ya dame ta, sai gudawar da tayi, kafin gari ya waye ta wartsake, ai kuwa wurin karfe tara yana kitchen yaga ta nufi firji din, dauke kai yayi, domin riga da zani ne a jikinta ya mata kyau, ta dauki kofi zata tsiyayo zumar ya rike hannunta. "Kul ki kuma sha kin ji ko?" Ya fada mata yana dan haɗe rai. Komawa tayi da baya, idanun ta suna rau-rau. Share ta yayi ya gama abin karyawan ya ajiye mata taci amma fir taki, sai da ya kira Ummi domin kukan banza take mishi. "Me ya same ta?" "Ina zan san mata, meye kuka zuba a firji tunda ta samu taki abincin karyawan sai shi." Ware idanu Ummi tayi tana faɗin." Ke ba abinci ba ne, magani ne na gyaran jiki." A ransa ya ce. *ai ho shi yasa ni da nace na so fadawa duniyar tarzoma, tow kuwa ta gama cin maganin kwashewa zan yi na kar ɗakina, sauran kuma sai ta samu lafiya taci haka kawai, a nime a lalata min tarbiyyar da aka gama bani* ban dai Ummi ta rarrasheta. "Gaskiya irin wannan abin a daina bata, domin da ace na biye mata munci tare me zai faru." "Ubana dadina da kai baka iya karya ba, domin kuwa gashi nan ka fada min kunci jiya ko?" "Ina ina? Ai daga ganin su nasan ba kayan Arziki ba ne, rufa min asiri." "Baba na nasan halin ka, kai ma kwadayayye ne irinta ka sha wallahi " "kai Ummina me zai saka na sha!" Zai mike ta ce mishi. "Tace min tare kuka sha " "amma ai kadan nasha" ya fada yana barin falon, dariya Ummi tayi, sannan ta rarrasheta ta karya, ta ce mata ba kullum ake ciba, kuma yana saka ciwon ciki. Gyada kai tayi. Bayan kwanakin da suka biyo baya, Sa'ade da Abuturab, kamar wasu abokai ne ko sa'ani, domin wani irin sabo ne a tsakanin su, wanda ta saka dole ka fahimci ba iya soyayya ba ce, har da kulawa, ranar da aka koma da ita asibiti aikin farko hatta Inna sai da aka gaya musu, su saka su a cikin Addu'ar su. Ayi aikin cikin nasara. An fara aikin tun karfe takwas na dare, ba a gama ba, sai karfe hudu na asuba, sannan aka fito da ita, an daure kunnen baki daya. Har dakin ta Ummi ta kaita, kusan ita ce a jininta,sai Hajiya Kudirat tana waje, lokacin da Abuturab yaga har lokacin tana kwance, sai da jikinsa yayi sanyi, bata farka ba kuwa sai karfe shida a yamma har sun cire rai, domin wani irin tsoro ne ya kama su. Koda ta farka wani alluran suka mata, domin ta farka tana kuka ne, domin zafin ciwon. Sai da ta kwashe kwanaki biyar kafin ta fara dawowa dai-dai. A lokacin Ra'is ya zo ya ganta, sai dariya yakewa Abuturab. *** A can kwara kuwa, kwanan Hajiya Daulah biyar ta dawo sokoto, domin ta zauna da Sultanate ta fahimci zata iya karawa da Ummin su, don haka take kara shiri sosai. Kallon Number Abdul yayi wannan shine number Abuturab, ya kara nanatawa a ransa. Kafin ya kira Abuturab. "Ka sake min Mata ta domin da ni ta dace ba kai ba" ya fada cikin matsanancin fushi, Dariya ya fashe da shi irin dariyar da ake kular da mutum ya ware idanun shi ya ce. "You already done a big mistake, domin ban fara son Lucky ba sai da na koyawa dangina sonta. Kai hatta matar da na aura sai da na koya mata soyayyar fulani. Sannan ni namiji ne, bana haɗa soyayyar uwata da soyayyar macen da nake so, kuma ban fara sonta domin na karya mata zuciya ba. Har abada ba zan tab'a sakewa ta bar inda nake balle har takai da na sake ta. Soyayyar lucky gaskiya ce lallai gaskiya ce ina tausaya maka domin Tabbas ganin mu a tare shine ajalinka. Kuma kaji a ranka ko sau dubu zaka kira ni kalama daya zan baka ba zan sake ta ba " (Su kwaila anyi kasuwa how market) #Mai_Dambu [08/07, 7:16 pm] usmanlauratu71: 59..... UK, kallon yadda ya hada mata abinci yake, cikin rarrashi yake bata. A hankali take amsa, domin babu damar motsi da karfi ko tauna da karfi, abin da ya hada kunne da gangan jiki ba wasa ba, yadda take motsa bakin ya sa shi shagala da kallonta. "Mara mutunci ashe wa kanka kake gyarawa hanya shi yasa da nace, ina so kayi ta danna min ashar baka da imani!" "Na zata a gidan ku ake rabawa, zanci uban ka." Ya fada yana bata abincin. "Wallahi baka da kirki." Juyawa yayi son magana, amma kuma ya fasa ya kama motsa bakinsa, yadda Ra'is zai fahimci ba karamin zagi yake mishi. "kayi hakuri ka fadi abin da yake ranka, wannan motsa bakin gara ka rufe ni da duka." Banza ya bawa ajiyar sa, can ya kasa hakuri ya ce mishi. "Hmmm! Yaushe zata fara jin magana?" A dan fusace ya kalle shi, "hakuri " ya fada yana kallon yadda yake bata abinci. Turo kofar dakin Ummi tayi da Hajiya kudirat. "Ra'is biye mishi kayi ka zauna anan, bayan kasan yau zamu bar garin?" Juyawa Abuturab yayi yana kallonta a marairaice. "Ummina " abin ya motsa. Sake baki tayi tana kallon sa. "Baka girma ne?" Rau-rau yayi da idanu sai ka rantse da Allah baby boy ne. "Baba karami zan saɓa maka, kai yaro ne?" Idanunsa ne suka cika da kwalla. "But" zuba mishi idanu tayi, cikin ladbatarwa. Sosai ya sunkuyar da kansa. Fita Hajiya Kudirat tayi tare da Ra'is don ta lura da Ummi tana son magana da shi. "me yasa baka da girma ne?" Kura mata idanu me cike da kwalla yayi. "Idan ka sake tears din nan ya zuba sai na tafi da Dearly na rantse da Allah. Mene ne?" Ta tambaye shi cikin rarrashi. "Kawai ina jin akwai wani abu ne da zai faru, idan kika tafi kika bar ni." Takawa tayi har inda Sa'ade take zaune. "ka saka a ranka babu wanda ya isa cutar da kai ba tare da Allah ya rubuta cikin ƙaddaran ka ba." Sunkuyawa tayi ƙasa ƙasa ta ce mishi. "Ko kuda ba zan tab'a barin ya sauka a jikinka ba, domin kai ne kwarin gwiwata." Gyada kai yayi yana kallon kasa, "Kar ka sake kace zaka biyo bayana matukar ba gama aikin aka yi ba, ka nutsu akan matar ka, zan roki Allah ya kare min ku."gyada kai yayi yana jin wani irin yanayi mai dadi da faranta rai. A hankali ta isa wurin Sa'ade ta rungume ta sannan ta janye jikinta tana faɗin. "Allah ya baki lafiya, ina jiran ki kinji!" Gyada kai itama tai, tana murmushi. Da haka suka yi sallama, so take ta isa akan lokaci. A gidan kuwa, sun hadu da Latifah wacce ta koma kamar munafuka, mika mata wasu takardu Ra'is yayi, ya ce mata. "Ki duba a hankali, zaki fahimci dalilin da yasa Ummin mu take son ta ji gaskiya daga bakin ki." Bata karba ba, ta ce mishi. "Ai na gaya maku ban san kome ba, idan kuka dame ni zan shigar da karanku." "Ranki shi dade, ba sai kin ga haka ba." Tsaki tayi tana faɗin. "Kar ma ku dame ni." Ta fada Allah ya gani sai ta ga karshen auren Abuturab da Sa'ade. Ba zata yi saki na dafe ba. Shi yasa take kaucewa kowa domin shirinta akan abuturab ne. Idan ya mai da ita zata gaya mishi wanda yake farautar rayuwar su, amma yace ba zai mai da ita ba zata iya dawowa da karfin tsiya. A daren ranar Ummi suka bar garin london, ba wai don Hajiya Daulah ba, sai dai rigima da Sultanate ta bude na lallai ala tilas sai Ummin ta kare kanta na boye shi su gaskiyar auren Abuturab da Sa'ade, idan ba haka ba sai dai kuma ya auri budurwa dal. Dalilin wannan tashin hankalin Sultan ya bukaci ta koma ya rasa yadda zai yi da Babarsa. Kwara. Daga Sultan babu wanda yasan Ummi zata dawo, domin kuwa bata fada ba ko Yaranta bata gaya musu ba. Asalima shiru tayi, sai da aka yi ta ganin masu aiki daga ɓangaren Sultan suna ta kaiwa da komowa. Koda aka tambaye su sai suce aiki kawai aka saka su. Don kuwa Ummyn Aymana tana gidan ita Sulta ya kira. An ce kowani mutum yana da tasa jarabawar, shi ta ɓangarensa Mahaifayar sa, zaune yake a gabanta. Sai tsagalgale shi take da masifa. "Hmm! Badi'atul Noor tafi ni a wurinka ko? Har tana da ikon yanke hukunci ba tare da shawarar elder na emirates council ba? Ita waye da zata saka Abuturab ya saki Latifah? Wato kai da matarka kun mai da ni yar banza? Shi wancan Yaron da dan gatan ku ya raba shi da Matar sa anyi mishi adalci kenan?" Sai kuma ta kwantar da murya ta fara kokarin ganin ta shigar da manufar ta. "Tunda har haka ya faru, kuma an raba shi da Mansurah why not ayi duba da sarah tana son shi. Kuma nasan zata zauna lafiya da ita yarinyar da ya aura, koda yake amadadin a lalata mana suna da al'adar mu, zaka iya fahimtar da Badi'atul Noor ta saka baki ya rabu da ita, ba matar aure ba ce domin sun sabawa alada da tsarin mulkin masarautar nan, ita kanta yarinya taya zata yi solve din matsalar masarautar nan? Infact abubuwa dayawa da baki yake bukatar fada, amma kuma dole sai dai Yaren Kurame." Shiru tayi ganin har lokacin kansa na kasa, bai ce mata cikanki ba. Ta ja gwauron numfashi ta ce. "Hmm! Bansan me Badi'atul Noor take son nayi ba, duk da hakura da nayi tana zuba ikonta sai dai ba zan lamunci kace zaka sadaukar da kujeranka ga Abuturab ba, a jira dai Allah yayi ikonsa yawwa domin na fahimci kome." "Umma wallahi daga Badi'atul har Abuturab babu me tunani akan kujeran da nake, Umma ki gane Badi'atul Noor bata da ra'ayi akan mulki ko wani abu, don Allah ki daina fadar haka akanta." Gwalallo idanu tayi cikin madaukakin mamaki ta ce. "Hmmm! Ka zata bani da sani ne akan mutanen yau? Meye basu yi kamar ba zasu yi ba. Allah na tuba ba dai ayi sha'anin na birni ya cuci na kauye ba, yanzu abin da nake so, ka sa Abuturab ya shigar da maganar auren Sarah ubanta sarki ne wan ka, kaga kenan zata haifa mana zuri'a dayyiba." "Umma idan Badi'atul Noor tazo zan kawo ta, sai ki mata bayani yadda zata fahimta wallahi ba zan iya tashin hankalin ta ba." "Laaaa tsoronta kake ji? Kawai ka gaya min tsoron ta kake ji, shi kenan tunda ban isa da kai ba, Badi'atul Noor ta isa da kai ai, ba kome na haifa mata fatari yasaka ta juya ka son ranta, ni da na haife ka ban isa juya ka ba." "A'a Umma ba haka nake nufi ba, bana son kina cusa kanki cikin hidimar Badi'atul Noor ce, amma kiyi hakuri zan duba kuma zan tuntube Aliyun, amma idan ya ce baya son ayi hakuri Yaran yanzu ba a musu dole ba, sun bata zumunci balle an musu dole." Sake ballo wani rikici tayi yayi ta lallabata amma baki daya ya kasa fahimta, sai da aka kira shi yayi baki ya kyale shi tana kara cika tana batsewa, kuma dole Badi'atul Noor ta saka Abuturab sake matarsa. The following day, Ummi suka iso da Ra'is sai dai baki daya bata samu haduwa da kowa ba, domin ta kwaso mura me shegen karfi, wanda ya tilasta mata isolating kanta na wani kwanaki. A hankali ta samu like five days, sannan ta amsa kiran Sultan. Bayan ta zauna tana kallon shi, idan ka kalle shi zaka fahimci yana cikin damuwa sosai, amma fuskar shi taki nuna haka, tana saurin fahimtar damuwar shi daga yadda yake yawan kura mata idanu ne, haka yasa ya ce mata. "Your highness kana lafiya kuwa?" Ajiyar zuciya ya sauke ya ce mata. "Queen Mother, ina cikin damuwa." Ya kwashe mata kome ya gaya mata, sannan ya yi shiru yana kallon yadda fuskarta zata dauka, sai yaga bata damu ba, sai daukar apple tayi tana ci tana kallon tv."baki ce kome ba?" "Eh toh me zance.?" Ta kuma tambayar shi, "i thought you would said something?" "Ko daya, is oky idan suka tunkare ni, amma basu tun kare ni ba, babu wanda zan mai dawa magana. Itama Daulah ina jiranta shi kenan ai" shi a tunaninsa zata d'aga hankalin ta ne, sai yaga bata damu ba.don haka ya bar zancen. Wasa wasa Sultanate tasan Ummi ta dawo amma ko da wasa, bata yarda sun hadu ba, domin tana fada cewa Badi'atul Noor ba mutu ba ce, ita kanta bata ragawa kanta ba, balle wani don ko tafiya take kamar akwai masu taka mata baya, asalima kamar aljanu na.mata hidima ne. Shi yasa taki yarda ta hadu da Badi'atul. Sai da Ummi tayi sati biyu sai ga Hajiya Daulah, domin koda Ummi ta dawo rumor's din da ake a cikin masarautar yana yawo. Da Hajiya Daulah ta iso baki daya a bangaren Sultanate ta sauka. Hajiya Suhailah tana kallon su, aka rasa wnada zai kuskura ya tunkari Badi'atul Noor da zancen sake Sa'ade...(😂😹🤣 wai me suke nufi happy weekend 😬😂) #Mai_Dambu [09/07, 8:02 am] usmanlauratu71: 60.... Tun daga nan Hajiya Daulah ta fara gane how Badi'atul Noor take domin, bata ganta ba amma kuma ta fahimci yadda kowa ke shakkar, har ta kwana ta wuni Sultanate bata ce mata kome ba, karshe da ta gaji ta ce mata. "Ranki shi dade, ina ta jiran ki akan al'amarin Abdul baki ce kome ba." "Kin san ba zai yiwu na tunkare ta ba, amma ke zaki iya idan yaso sauran goyon bayan zan baki." Sultanate ta fada tana kallon ta, don ita kanta Badi'atul Noor ba kyaleta zata yi ba, ai kuwa haka aka yi. Bayan sun gama magana wurin la'asar aka tura a kira Ummin, tana tsaka da waya da Abuturab, sai da ta gama waya sannan ta cewa yar aikan. "Kice ga ni nan zuwa." Sai da ta b'ata lokaci kafin ta shiga ɗakinta ta shirya sosai, ta kure a daka. Tana fitowa ta kira Ra'is. "Kana ina?" "Ina tare da Sultan a fada." "Madalla Wazir karami" "Na gode Ummina." "Allah ya muku albarka." "Amin Ya Allah" kashe wayar tayi ta nufi part din Sultanate, kure wanka tayi yadda baki daya ka ganta sai ka firgita. Tun kafin ta isa falon masu kula da bangaren Sultanate suka yi ta zubewa suna gaishe ta. Har ta isa cikin falon, zama tayi a daya daga cikin kujerun falon. Ta sakar musu murmushi sannan ta kalli fuskar Sultanate don ita aka ce tana kiranta, "Allah ya baki lafiya da nisan kwana gani, da fatan na same ku lafiya!" Tabe baki Sultanate tayi tana faɗin. "Lau tunda har kika iya gaban kanki ba, ashe kuma kin saka Aliyu ya sake Latifah inji ba kamata yayi tana ha'intar auren shi ba? Kuma ba laifin kisan kai tayi ba?" Murmusawa tayi ta ce. "Eh tow ta wannan bangaren sai dai nace miki, hurimin na ne da d'ana, ha'inci da kisa basu kai girman laifin da zai saka nace Abuturab ya sake ba, sai dai ina iya yafewa mutum amma bana yafe cutar min da Y'ayana!" Wani irin kallo Sultanate ta sakar mata tana faɗin. "Shi Abuturab din hala jariri ne da za a cutar da shi, dadin abin kun fi kusa da Uban Yarinyar.". "shi yasa nake mamakin yadda wasu suke mana katsalandar s cikin matsalar mu, tunda bata shafe su ba." "Allah ya baki hakuri, kin sai dai nice na haifi Uban Aliyu" dauke kai Ummu tayi tana murmushi ta ce. "Eh shi yasa nake jadadda miki ni ce na haifi Aliyou, kuma ni keda ikon saka shi na hana shi, ai ba laifi ba ne koya min aka yi." Harara Sultanate ta watsa mata tana cewa. "Na tura sako fada, domin ba zai yiwu ki saka Aliyou ya auri matar wani ba, domin aure ne akan aure. Sannan nayi magana da Dauda na Jama'a, zai duba al'amarin aure tsakanin Abuturab da Sarah, na yanke shawarar." "Shawara bata karbu ba, Ummu Mansurah babba, ni Badi'atul Noor nace ba zan saka Aliyou ya sake matar shi ba, auren shi bisa ka'idodin addinin musulunci aka yi, sannan kuma aka tabbatar da haka, batu na Dauda ya duba yiwuwar auren Sarah da Aliyou na sake, duk wanda ya sake ya saka kansa cikin maganar sai na kure mishi hadda." "Dole d'anki ya sake mana Sa..." A fusace Badi'atul Noor ta daka mata tsawa. " Ki min shiru!" Ta bude mata golden eyes dinta, hàdiye yawu tsoro Daulah tayi tare da kasa da kai. "Ba dake nake ba, da ita uwar gayyar nake, kul ina magana ki jefa min baki, baki isa ba wacece ke? Me kike da shi. Na kuma magana ki saka min baki sai na saka an rufe min ke wallahi" sannan ta juya ga Sultanate tana murmushi ta ce. "kar ki damu Uwata, da ita nake ai ba zan miki tsawa. A ina muka tsaya ma?" Tsabar ta tsorata bakinta yana rawa ta ce mata. "Ai kin ce ba zai yiwu ba, kuma na fahimci haka Badi'atul Noor" murmushi tayi ta kalli Daulah. "Da ace tun farko kin dauki rayuwar Yaranki da muhimmanci ba zan tab'a goyawa Baba karami bayan auren ta ba, amma baki daya a duniya lallai so kike a san ke wata ce, ke din banza idan kin mutu a ina za a saka ki rami, sannan kar ki sake ki kara kwana a gidan nan akwai mota zai mai dake airport kar na kuma ganin ki, soka ki za ayi a cikin rigimar da kullum ba karewa xata yi ba. " Gyara zama Ummi tayi ta daura kafa daya akan daya ta ce mata. "Kin ga same ? Yara biyu na rasa lokaci guda, tsakanin su kwana bakwai. Duk da haka ban tab'a kawowa zan manta abin ba, na rasa Yayata da nake bi ita da D'anta babban dan gidan nan, ita Yayata da cikin wata tara. Kin zata na yafe ne? Ina sane, don haka ki koma gida ki karfaffa d'anki ya tsaya da kafar shi, Sa'ade ba matar shi ba ce, sannan ya koyi son abin da yake rabon shi ba kwadayin ba. Gidan nan da kike gani illarsa ta fi da gamsheka domin idan da nisan kwana ya sare ka zaka rayu, a gidan nan idan aka sare ka dai ka mutu. Sannan ina son my baby boy I can let him go down like that, kin fahimta duk wanda ya sake ya shiga al'amarin Aliyou wallahi sai na batar da shi ko uban Aliyou ne balle wata ko wani, im always protect my baby boy, don haka ki saka kafa ki bar gidan nan, Allah ya bawa Abdul mace ta gari, idan kuma kina da wata magana kiyi." Ta fada tana kallon Sultanate da tayi tsuru-tsuru. "Sultanate baki jin dadi ne?" Mikewa tayi da sandarta. "Zan kwanta ne kaina yana ciwo" "ki sha magani kafin ki kwanta " sannan ta juya ga Hajiya Daulah da jikinta yayi sanyi sosai, don maganar Ummi ya shige ta. " Ita uwa tana amsar duties dinta na uwa ce daga ranar da ta zama mace, daga ranar da ta san tana dauke da wani abu a tare da ita, zata kara zama uwa cikakkiya, adalcin da uwa zata yi ta samawa danta Uba na gari, haka shi ma Uba, adalcin da zai yi ya samawa dansa Uwa ta gari. Baki san gwagwarmaya akan Yara ba ne, domin da kin sani ba zaki tab'a takowa har nan akan matar da bata son d'anki. Da kin san lokacin da uwa take hana idanunta barci domin rayuwar Yaranta ya inganta ba zaki tako nan ba, bana fatan ko da wasa wani yaji kuncin da na ji, amma xan baki shawara ki tsaya akan matsayin ki na uwa ta haka ne d'anki zai zama a tsaye koda baki nan, ina son Yarana da yawa, so ni ba zan tab'a hana so kome ba, matukar bai sabawa Addinin Musulunci ba. Da wannan nake baki shawaran kar ki sake barin wani yayi amfani dake domin maslaharsa." "Na gode sosai, na gode sosai." Ta fada tana mikewa, itama Ummin barin gidan tayi sai da ta nufi part dinta ta kira Ra'is ta ce ya je ya dauki Hajiya Daulah ya kaita airport. Tow ya ce. Bayan barin ta gidan Sultanate ta fito zata tari Daulah. "Ke munafunci ne ki bari na kara gwada. " "Me zaki gwada? Tunda uwata ta haife ni ba a tab'a min tsawar da naji shi kamar aradu ce, idan akan matar danta ne da danta na hango zata iya kome, dayawa cikin maganganun ta sakonki ne, don Allah kyale ni kar ki saka ni cikin tashin hankalin ku, na gano inda na gaza akan Yarana." Take jikin Sultanate yayi sanyi, wato ita Badi'atul Noor, duk wanda ta zauna da shi sai ta asire shi da magana, tana ji tana gani Daulah ta tafi, kuma ta kasa kome abin ya dame ta, yanzu tana ji tana gani mulki zai fita a hannun danta. *** UK. Zuba mata idanu yayi, tea take sha a hankali. Yau da a warware kunnen, sai kallonta yake kurban tea ɗinta tayi ya ɗan tab'a saman bakinta, kallon bakin yayi. Murmushi yayi ya kai hannun shi yana shafa saman bakinsa. Bata gane ba, ya kuma shafawa bata gane ba. Mikewa yayi a hankali ya kai bakin shi ya cafke baƙin nata, ya fara tsotsa in gentle, shi da ya je goge wurin zak'in sugar da yake saman bakin ya rinjaye shi, bai san lokacin da ya shiga lalubar bakinta baki daya ba, niman harshenta yayi cikin wani irin nutsuwa da shi kansa, bai tab'a zatan yana da ita ba, hannunsa daya ya kai bayan ta, sannan ya samu itama hannunta dukkan biyu suna rike da rigar shi, so take ta kwace bakinta domin ji take, kamar zai cinye mata bakin gabakidaya, haduwar harshen shi da nata, ya haifar masa da matsanancin ƙishirwan da yake ji, shi kansa jin wani irin mazantaka yake tana fisgar shi, amma haka yake calming kansa, tare da tsayawa iya nan, sai da ya kai kusan minti sha biyar a iya French kiss, kawai kafin yayi broke kiss din, ashe har da guntun kwallar ta, domin wannan shine first time da aka yi kiss dinta, sunkuyar da kai tayi hawaye na zuba, tun farkon fara abin ta sake mug din tea ɗin a kasa, karar shi yasa Latifah lekewa lokacin da tazo duba yana nan ko ya tafi, sai dai ganin yadda yake kiss din Sa'ade ya tsaya a ranta, babu shiri ta rufe kofar tana jin wani irin yanayi yana fisgar ta, koda uban bala'i sai ta shiga tsakanin su. Ita kan Sa'ade kin kallonshi tayi karshe ma ban daki ta wuce abinta, tana zuwa ta rufe kofar da sauri tana kallon kanta ta madubi, shafa bakin tayi da sauri ta rintsa idanun ta. Wani budurwan kunya ce ta kama ta. Shima a dakin bai ga wani kuskure da yayi ba, infact matar shi ce. And yana da right da zai yi abin da yake so da ita, murmushi yayi yana kallon kofar dakin. A hankali ya gyara dakin. Har ta fito daga toilet din amma kanta a sunkuye taki yarda su hada idanu. Haka ya koma gadon ta zauna, zama yayi a kujeran. Shigowar Drs din da suka yi aikin yasa ta mikewa ta zauna. A hankali suka zauna aka fara tattaunawa kafin aka shiga kunce kunnen, ana kunce daurin wani irin kara kamar an buga kararrawa yasa ta rike kunnen tana fashewa da kuka, rungumar ta yayi tana rike da kunnen. "congratulations, aikin yayi kyau sosai saima fatan sauki" wata nurse ta matsa tare da cire hannunta da jini ya bata, ta tura mata device. "Wannan zai taimaka mata kafin kunnen ya warke, amma aiki yayi kyau. " "Thank you" Abuturab ya fada. "Zuwa jibi zamu sallame ta, sauran aikin sai sabon wata gaba me kamawa. Ka shiga da ita cikin mutane domin device din ya zuko mata hayaniyar mutane. Haka zai saka ta saba da mutane da kuma makaranta." "Na gode " bayan fitar su ne, ya cigaba da rungumar ta. Hannun shi ya kai bayanta yana shafa bayan, tayi lub a kirjinsa. Yarinyar nan bata san yadda take narkewa a jikinsa kashe shi take da rigimar ta ba, haka ya lallabata har tayi barci, yana gyara mata kwanciya Latifa ta shigo. "Abuturab ina son ganinka" kallon ta yayi sannan ya ce mata. "Ok Ina zuwa!" Ya dauki coat dinsa ya bi bayanta, har waje can, zama suka yi ta kalle shi. "Dama akan abin da ya faru ne, ko zaka maida ni zan gaya maka gaskiya abin da baka sani ba " "bana buƙatar sanin kome, tow wai ma me zan sani bayan kin rena kowa akan abin da kika sani " "ina son ka zan gaya maka gaskiya amma firstly ka mai dani dakina." "Sai dai ki samu Ummina." "Zaka mai dani dakina koda Umminka bata sani ba" ta kai bakinta kamar zata sumbace shi. Saka hannu yayi ya tare ta. "ban yi wannan girman da zan yi kome gaba gad'i ba, sai da iznin Mahaifiyata.. #Mai_Dambu [10/07, 9:07 am] usmanlauratu71: 61.... Kwara. "Hajiya kamar na sanki?" Ra'is ua fada yana gyara madubin motar, zunzurutun iskanci. Ya kuma juyawa ya kalleta, "huh wace ce kema?" Banza ta mishi tana kallon window waje. "Huh Hajiya Daulah?" Ya fada yana murmushi. Wayar shi ce ta yi kara ya ɗauka tare da sakawa a handfree ya ce mata. "Barka dai Ummin mu, gatar mu the great queen Mother." "Ka ɗauke ta?" "Eh Ummina ina zan kai ta?" "Airport ka kai ta cikin amincen Allah!" "In sha Allah, ai guest din mu ce, za a kaita cikin amincin Allah." "Allah ya maka albarka." "Amin Ummina" ta kashe wayar. Sake kiran shi Ummi tayi, ta ce mishi. "Kada ka mata magana, itama Uwa ce domin nasan halin ka da shegen tsokanar tsiya " "tow Ummina " ya fada yana murmushi. Kashe wayar ta yi, yayi ta dariya. Wato Ra'is baya jin magana sam, domin figar motar yayi a guje. Ware idanu hajiya Daulah tayi tana faɗin. "Kai Yaro! me na maka zaka hallaka ni?" Smirk yayi irin emojin din nan ya ce mata. "a'a baki min kome ba, domin kuwa Ummi tace na kai ki da amincin Allah ." Haka yayi ta gudun ganganci a garin, sai da ya hautsina mata lissafi sannan ya koma gefen hanya ya tsaya da sauri ta buɗe motar ta fara kwara amai, murmushi yake yana faɗin. "Ki godewa Allah Ummi tana da lissafi da kirki sosai, da ace wata ne sai na kusan watsa ki a cikin rami " "Amma ina jin tace maka." Murmusawa mata yayi ya ce mata. "ke da kika zo kina Nana hauka a cikin gidan fa? Har Abban mu ya ce ga abin da ya dace ki ce a"a. Mafi girman kuskuren da zaki kuma aikatawa, shi ne kara kwaso kafaffunki da sunan a kashe auren Future's king da matar sa, sai na taka mota na kai ki bakin dam kin fada cikin ruwa, babu abin da ya dame ni." Shiru tayi ya koma cikin motar ya cigaba da janta. Har airport ya kaita, ya mata kome sannan ya juya ya kalle ta. "Ki cewa Abdul ya koyi hakuri da abin da yake da shi, domin mu ma da muka fito wancan gidan haka muke hakura da abin da muka samu, saboda koda gaskiyar ka, sai an kashe ka. Mahaifina yana raye amma saboda gaskiyar da yake son ta rayu yayi karyan ya mutu, idan har saboda gaskiya zaka zabi mutuwa, me kike tunanin zai faru da kike kokarin saka kanki cikin hidimar masarautar nan? Kin ga Ummin mu har yau yayanta basu da ikon watayawa a cikin masarautar nan domin rayuwar su farautar ake balle ke da son zuciya ya kwaso ki, don haka zan baki Shawaran karshe kar ki kuma zuwa masarautar nan da sunan wani abu, idan ba alkhairi ba shima ki zauna iya inda kike son tsira da rayuwar ki da ta d'anki." Kamar wacce aka watsa ruwan sanyi, haka tayi tsamo-tsamo. Har ta juya zata tafi ya ce mata. "Kome da kika ganshi a duniyar nan a rubuce yake." Daga haka ya wuce bata ce mishi kome ba. Sai da yaga tashin jirgin su hankalinsa ya kwanta. Sannan ya juya yana me wucewa wurin motar sa. A bangaren Ummi kiranta Sultan yayi ya tambaye ta, me ya faru. Murmushi tayi ya ce mishi. "babu wani abin da za ayi domin na kwantar da tarzoman su." "Na gode sosai, kin yi min abin da na gaza yi, kiyi hakuri ɗazun na tura Ra'is da soke maganar Abuturab ga Dauda na Jama'a." "Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana." Ta fada tana kashe wayar. *** Kallon ta yake yana mamakin halinta, "Zaka iya mana, nasan zaka iya ka dawo da ni dakina " shiru yayi yana kallon ta, bayan ya gamawa Lucky alkawarin daga ita babu wata mace. "Ok bani wasu yan kwanaki zan yi nazari, idan mai yiwuwa ce zan gaya miki idan ba mai yiwa ba ce zan gaya miki." Daga haka ya juya abin sa. "baka son gaskiyar da zan gaya maka ne?" Murmusawa mata yayi sannan ya ce. "Bana bukata." Ya fada yana wucewa dakin da Lucky take, a hankali ya shiga ya shafa kansa yana me Ciro wayarsa ya tutturawa Ummi sakon Latifah. Turo mishi sako tayi, da cewa. *Duk yadda zaka fitar da Sa'adatu kar ka sake wani abu ya cutar da ita idan ba haka zaka ga fushina.* _in sha Allah haka ba zai faru ba_ kallon Sa'ade yayi d bata san me ke faruwa, takawa yayi har gefenta ya zauna, yana me kallon hannunta da yake dauke da zanen lalle. Saka hannun shi yayi ya sarkafe da nata. Sumbatar hannunta yayi, wani deep warm kiss ya sauka a hannun. Kiran wayar shi Ummi tayi. "Na'am Queen Mother" ya fada yana karawa a kunnen shi. "Ummi na rike kaina domin Sa'adatu ne, bana son na zauna da wata mace bayan nasan ita kawai nake muradi, idan kuma wani abu." "Shi yasa na gaya maka, kome zai iya faruwa tunda, zata dawo ne domin daukar wasu abubuwan da ko karasa abin da bata magana ba. Kar ka sake alakar ya haifar da abin da zai saka Sa'adatu kuka." "In sha Allah babu abin da zai faru." Ya kashe wayar yana kallon Sa'ade da take wasa da yatsun hannunsa da ya sarkafe da hannunta. Haka suka zauna shiru yana jin wani irin dumi daga jikinta yana shiga jikinsa. "me kike bukata? Ni naki ne!" Gyada kai tayi cike da kunya, domin baki daya ya sata jin kunya, ko ba kome yanzu tana jin muryansa sosai. Ajiyar zuciya ta sauke tana me soke kanta a gefen kafadar shi. Janyota yayi jikinsa yana shafa bayanta. Sake lafewa tayi a jikinsa kamar mage, yana jin Tudunwadarta a jikinsa wani irin abu yaji kamar ana tsikara mishi allura. Matseta yayi da hannu daya, yana me kai ɗaya hannun saman cinyarta zuwa cikin rigar ta, shi kansa kamar ana ingiza shi, ya shiga bin tsarin kome na cikin yana tabawa, musamman cibiyarta, lumshe idanunta tayi da mugun karfi tana jin kamar anan jijjiga duniyar ta, iya tafiyar tsutsa yake da wurin. A hankali yake matsar da hannunsa, har zuwa na Fulaninta. Wani irin numfashi ta ja, da sauri ya zuba mata idanu, ganin yadda ta rike rigarta gam yasa shi fahimtar sakonninsa suna da tasiri sama da fada a baki. Jininta da jikinta ne suka dauki wani irin dumi da rawan sanyi, musamman da ya kasance al'amarin ya kai kan Tudunwadarta ta. Jikinta sai wani irin rawa yake, shi kuma bai fasa kaiwa da komowa ba. Hawaye ne yaga na zuba a fuskar ta, domin shima ya manta inda suke. Yana shirin wuce makadi da rawa. Harshen sa ya saka yana lashe hawayen, har cikin kwarmin idanun da ya tsotse ruwan hawayen. A hankali ya sauko da kansa zuwa karan hancinta, tsotsar karan hancin yake kamar wanda ya samu wani alewa, ya sauko kasan hancin zuwa bakinta, rike shi tayi gam, domin hannunsa bai dai na abin da yake ba, wani abu take ji kamar tana fitsari ne oho, ko motsi jikinta yake yi bata sani ba. Ta san dai baki daya kashe ta yake da wani abun da bata tab'a barin Abdul ya mata ba. Kamar yadda yake bayyana mata kome, haka take rike da rigarsa har lokacin. Bakinshi ya kai habbatarta, ya shiga cinye habbar har zuwa wuyar, tashi yayi daga zaune ya tsaya a gabanta, jikin shi yana wani irin rawa, ya shiga bude botirin gaban rigarta. K'amk'ame shi tayi, tare da sake rintsa idanunta. A zafaffe ya shiga ya motsa ilahirin garuruwan da suke tare da ita, babu kauye da gundumar da bai kai kansa wurin ba, kamar wani zautacce haka ya koma mata, sai da yaji sautin kukanta yana tashi yasa shi janye hannunsa, ya kai hannunta saman shugaban karamar hukumar shi ya daura a kai. Bata bude idanu ba, har ya bude zip din wandon ya saka hannunta a kai, da sauri ta ware idanun ta, ta ga abu bata san lokacin da ta fashe da sabon kuka ba, tare da saka hannu a bakinta, jikinta yana rawa. Rufe idanunta tayi tana kuka, mai da zip din yayi ya gyara mata rigarta. Ya zauna yana me rungume ta. Ina zai iya wannan abin da ya taso masa, wato dan janyota jiki da yayi ya haifar mata da wannan tashin hankali. Dakyar suka rabu ta fada mata tayi wanka da tsarki, bayan tafiyar shi tayi wanka, kamar Latifah tasan da tafiyar shi, ta shigo ganin yadda Sa'aden take goge gashin kanta da towel. Kallonta tayi cikin sakin fuska ta tambaye ta, da sign language ta ce mata. "Kina nan dama?" Wani irin kallo Latifah ta mata, tare da zama ta ce mata. "Ya akayi kika jika kanki?" Sunkuyar da kai tayi, me zata ce mata. "Wani abu ya shiga tsakanin ku da Prince ne?" Ta tambaye ta, a rude, kunya yasa Sa'ade rufe fuskar ta da towel. ranta yayi mugun b'aci. Tab'e baki tayi ta ce mata. "Kin san zai mai dani ɗakina kuwa?" Da sauri Sa'ade ta cire towel din, gyada kai Latifah tayi ta ce mata. "Ni nace yazo ya miki abun da yake min, kar ki damu akan ya kawo ki nan ya ajiye ki, ai tunda muka rabu kullum muna tare, yanzu ba gaji ne nace kema yana ɗebe miki kewa, domin bana kishi dake" gyada kai Sa'ade tai, ummi ta gaya mata matarsa ce, amma sun raba auren saboda wani dalili. Ganin ta jefi karamin kwanyar sa'aden cikin damuwa ta ce mata. "Kar ki damu ai ni ba zan zafaffa kishi akan sa, nasan duk abin da zai nima na kwana biyu ne zan ce ya cigaba da ɗebe miki kewa, kinsan dake bazawara ya auro ki wani ya gama bude miki idanu, ba zai samu gamsuwa dake ba, amma kin gani budurwa ya same ni. Na sha wahala a hannunsa, kun zawarawa ai kofar ko faci aka masa a bude yake kamar Rijiya " daga ta ficce a dakin. Zama Sa'ade tayi shiru, tana kallon kasa. Tun daga lokacin ta daukewa Abuturab wuta, kamar yasan wani abu ya faru sai ya ki niman makale mata, ranar da za a same ma. Latifah tazo tana wani shishige masa, kamar ya share ya sai ya kyaleta. Duk sa'ade tana kallon su. Prince yi min kaza, Prince duba min wayata, karshe yadda ta zauna dab da sji har kafad'arta ba gogan na shi, kallon su kawai sa'ade take yana yake. Har aka sallame ta, cikin wani irin jan aji ta kame kanta, ta koma bayan motar ta zauna tana yaki da zuciyar ta, domin wani irin kuka take ji, amma taurin kai da zuciya ya hanata kukan, ganin yadda ta kame kanta ba haka Latifah taso. A burin ta Sa'ade ta birkicewa Abuturab da hauka sai kuma haka bai faru ba. Har gida da suka isa bude motar tayi, ta wuce hanyar apartment dinsu, ta tsaya. Ganin yadda tayi tafiyar bata jira su ba, ya sa fita ya bude kofar gidan dake ana sanyi har da ƙanƙara. Sannan ya juya ya koma ya kwaso kayan su. Tunda ta shiga ta wuce ɗakinta bata kuma yarda ta bi ta kansa ba, gyaran ɗakinta tayi ta saka turaren wuta. Sannan ta cire kaya, tana kokarin daura towel ya shigo, da sauri ta daura. A hankali ya tawo har inda take yana kallonta. "Laifin me na miki!" Ya tambaye ta, yana jan towel din da ta daura, "ina kula dake, wato har kin san ki dafa mutum da ruwan sanyi, ni na taso inda ko murmushi kayi sai mun wurga ayar tambaya akansa." Ya ja towel din ya fadi a kasa. Ganin har zuwa lokacin bata yarda da kalle shi ba, sai madubin dakin take kallo, juyar da ita yayi tare da watsar da kome na madubin, ya daurata saman madubin. "me nayi da na cancanci haka? Baki tausayina ne da zaki na fushi da ni " ya d'ago ya daura saman dress mirror. "me nayi da zaki na min fake smirks a gabanta. Open your heart, ki gaya min meye a mind ɗinki. So kike Ummi ta saɓa min?" Ya fada bayan ya cire rigar shi. "yau kwana biyu ina lura dake, me yayi zafi?" Ya shiga bin duk wani abu na jikinta yana tab'a,cikin kulawa da salon kaunar shi me ratsa zuciya. Gashi bata da hakuri akan tab'ata ya fahimci ana taɓa sai kuka.bakinsa ya kai kunnenta. "Ba kuka nace ki min ba, meye nayi kike treat dina haka?" Ya kai bakin shi wuyarta yana lasa har zuwa fuskar ta. Kamar zai cinye mata fuska. Domin mahaukaciyar kissing yake mata, hannun shi dukka biyu suna kan na shanunta da suke mata zafi. Bakinsa ya kai kamar wani baby ya cafke sai da ta sake wani irin kara. Tana tura kansa yana kara manne mata. Bata san shi bane bata san waye Abuturab ba ne, fushinta ya saka yana son yaji duminta, yaji hau take fushi haka. Yadda take kokarin janye shi haka yayi cak da ita zuwa gadon su. Ya mata iyaka da wurin, baki daya ya manta ummi ta gaya mishi bata san kome a wannan duniyar ba, shi yadda yaga Abdul yake kulafucinta tunanin shi basa yayi hala ya tab'a zumar ce ya haukace rashinta, sosai ya shaida mata kome akanta. Ita wani abun da yake mata ma, ko a tarihi bata taba ji ba, amma qaddara yau yasa ta ganin abin kamar a mafarki. Ga babu baki balle tayi ta ihu sai kuka take da bata san na meye ba, bata taɓa sanin akwai abin da ya kai haka, shi yasa da ya fara wanin abin da yafi haka, kasa kuka tayi tana ture kansa a inda yake, ture shi take tana son ya kyale ta. Amma baki daya Abuturab so yake ya goge mata hadda, don bakin Jarabawa duk abin da suke akan idanun Latifah da hawaye ke zuba mata, kamar an dasata, tana kallon yadda Abuturab yake making love da yarinyar da bata kaita kome kome, ya zubda girman sa yana wani abu kamar dan iska, wato ita ce ma baya kauna, shi ne zai zauna yana kashe yarinya karama da abubuwan da ko ita babbar mace sai haka, kuka ya saka tana me toshe bakinta. Shima Abuturab din kamar yasan ko jikinsa ya bashi ana leken su ne, kashe hasken dakin yayi, musamman na gadon, domin itama Sa'aden bayan ta gama gyaran dakin kashe hasken yayi ta kunna iya dai-dai na jikin gadon. Sai yake shagalinsa tare da jin kamar ya cinyeta a a wannan ɓangaren, sai dai duk abin da yake iya haka ya tsaya. Bai nemi wuce sauran iyakar ba, musamman da yaga ta gama razana da shi, komawa gefe yayi yana me jan numfashi yana shafa fuskar ta. Domin taci kuka har ta godewa Allah, a hankali zai koyawa kansa yadda zai tafi da ita har duniyar maji dad'i...... (Fuck the enemies 🖕) #Mai_Dambu [11/07, 10:06 am] usmanlauratu71: 62.... Tun daga wannan ranar, abubuwa dayawa suka fara samun mazauni a hankali, domin dai shi yaki d'agawa Sa'ade kafa, sosai yake koya mata dabi'unsa da yadda yake, wadda har ta kai ita kanta, ta fara kokarin fahimtar abin da yake koya mata. A bangaren Latifah kwazazzaban ranta tayi tana ganin kamar Abuturab dawo da ita zai yi, bayan kuwa ba karya ba dawo da ita zai yi, asalima dauko wani hanyar wulakanci ya mata, shi ne duk yadda taso ta gaya mishi abubuwan da suka faru, fir dan batalikin nan ya ki amincewa. Asalima sai ya kasance basu zaman gida da Sa'ade, idan suka fita yawon buɗe ido suke da shakatawa. Idan kaga Sa'ade sai ka sha mamaki, ta kara cika duk da babu abin da kai shi bakin boda, amma ba tana shan murza irinta wanda yasan me yake yi, ga wani feshin love da yake koya mata, zuwa yanzu ta gane girman abin da yake mata, domin bini bini tana kwance a jikinsa. Ko tana makale a gefensa. Kamar yadda yayi alƙawarin sai ya cika rayuwarta da idanunta, haka ya cika Idanunta don idan yana gefenta zai yi wuya ka gane mata, yai Saturday, tana kwance a jikin shi ta bude idanu tana kallon yadda ya makalkaleta. A hankali ta fara janye jikinta yayi maza ya bude idanun shi. "Ina zaki?" Ya tambaye ta, mai da idanunta tayi ta rufe tare da daura kanta a kirjinsa, tana jin bugun zuciyar sa. Hannunta ta kai bayan shi tana shafa bayansa. "Shi ne nace ina zaki?" Bude idanu tayi ta ɗan matsa kaɗan zuwa fuskar shi ta sumbaci bakinsa. Irin unexpected din nan, shi kullum sai dai ya mata amma koda wasa bata taɓa kai hannunta ko bakinta da nufin ajiye mishi wani tarihi ba. Ware idanu yayi tayi maza ta janye tare da fadawa ban daki ta rufe kofar yana jin yadda take giggling, ikon Allah ya kai hannunsa bakin yana tab'awa. "Lallai yarinyar nan!" Ya furta a hankali, tashi yayi ya saka shirt ya nufi kitchen, ya fara kokarin gyara kitchen din ya share sannan ya daura musu abin karyawa, tana fitowa busar da gashin kanta tai da handry. Sannan ta nufi wurin kayanta ta ciro wata Flora skirt da whiter shirt armless. Sai craft veil da ta yane kanta da shi, oil kawai ta shafa a jikinta. Oud pur ta goga a bayan hannunta shafe jikinta da shi. Fuskarta kuwa dan hoda ta shafa sama sama, sai lipglow ta shafa. A hankali ta juya tana kallon dakin. Gyara dakin tayi tsaf ta cire zanin gadon da suka kwanta sannan ta shimfida sabo, ta dauki wanda ta cire ta saka a cikin washing machine, ta wanke shi. Sannan ta dauki zuwa bacloy na gidan ta shanya. Hango motar Latifah tayi ta d'aga mata hannu. Ita ta kwana biyu bata ganta ba, itama Latifah kallon Sa'ade take dake tana cikin mota ne, kura mata idanu tayi. She hate the girl, domin tana ganin ita ta mata iyaka da Abuturab. Baki daya a cikin abin da bai wuce sati biyu ba yarinyar ta sauya. Haka ta ja motar ta tana jin babu dad'i. Ita sa'ade bata san yanayin da take ciki ba, sai da ta shiga cikin gidan ta tuna da abin da Latifah ta gaya mata a asibiti, don haka tana shiga kitchen, rungumar shi tayi ya baya, tana murmushi sumbatar bayansa tayi ta juya tana kallon yadda fuskar shi ta yalwata da farin ciki, shaƙar kamshin abincin tayi ya mishi alamar (👌🏼) yayi. Dawowa gabansa tayi ta wani gefe can ta shiga tambayar shi, me yasa Latifah bata kwana anan? Kallonta yayi ganin sosai take son sanin wani abu. Bai boye mata gaskiya ba, ai basu tare. Shiru tayi kafin ta shiga mishi bayanin yadda suka yi a ranar, shiru yayi yana saurarenta. Kafin ya tambaye ta. "shi ne yasa ranar kika yi ta bani ciwon ka?" Tura baki tayi tana gaya mishi. "Tow cewa tayi ni bazawara ce, kuma ita ta tasa ka kula ni shi ne ba zan ji haushi ba." Idanunta ya kawo ruwa. Kwashe abinciin yayi ya kai falo, ita kuma ta gyara kitchen din, suna cin abincin ya kira Ummi suka gaisa, bayan sun gama ya ce mata, zai fita yanzu zai dawo. Yana fita asibitin ya wuce. Inda su Latifah suke zama, nan ya nufa yana zuwa ya riko hannunta suka fito daga yanayinsa ta fahimci akwai matsala, har wurin motar sa ya kawo ta. Ya bude mata ta shiga. Wato tunda Uwarta ta haife ta bata taɓa ganin fushin da ya bata tsoro irin na yau ba, asalin fuskar sa jajjur tayi yayi bala'i kamar zai dake. "Idan na kuma ganin ki da mata ta, wallahi sai kin gane baki hankali, kuma da kike tsammanin zaki yi amfani da ni ainasan kome." Daga haka ya kuma buga mata tsawa ta fita daga motarsa. Kamar munafuka ta fita, dakyar ta bar harabar. Can wani lungun asibitin ta Ni ma zama tai ta ci kuka sosai. Lokacin da ya koma gidan, ya samu Sa'aden shi tana ta barci. *** Sokoto Kwana biyu Hajiya Daulah ta dauka, tana jin ta wani iri, domin bata tab'a kawowa akwai wacce tafita bala'i ba. Sai da Allah ya hadata da Badi'atul Noor, duk sai ta ji kunya ya kamata. Bata saka Abdul a idanunta ba. Dirin mota ta ji zuciyar ta kamar zata fado a yan kwanakin nan tana fama da faduwar gaba. Turo kofar falon aka yi Afiyyah ce, fuskarta kamar wacce tayi hatsari da mota. Mikewa tayi tana faɗin. "Ke lafiya me ya samu fuskar ki?" "Ya sake ni Hajiya, Mahaifiyarsa tasa ya sake ni Bayan sun lakad'a min dukar tsiya " Ragwab Hajiya Daulah ta zube. Bata gama farfaɗowa ba, Aka kira wayarta Taufiq yayi hatsari, Yaranta da bata haɗa su da kowa ba, sai gashi jarabawar rayuwa da hakki yana bibiyar su. Dakyar ta iya tashi suka tafi babban asibitin sokoto. Kamar tayi hauka haka ta kira Dr Sharif da ya zare hannunsa akan Yaranta, Abdul ma tunda ya fahimci ba zata dawo mishi da Sa'ade ba, sai ya tattara ya nufi london domin ya dawo da matarsa tunda ita ta gaza. *** Kwara. Ummi da kanta, ta tura Ra'is har Sokoto ya biyawa Malam Aminu Umra tare da matansa dukkansu, sai mai gari da Malam Kalla. Wayyo Allah duk inda malam Aminu ya zauna sai ya faɗa. "Uwar mijin Sa'adena ta biya min umra, ai su din masu kudin kasar nan ne, ai ni yanzu nayi auren yar arzikn. Allah sarki Arzikin da naso ci da karfin tsiya yau gashi ina dangwalar da tsinke." Sai ya sake murmushi. "Wato yarinyar nan har abada ba zan kuma haihuwar irin ta ba. Domin dai gata nan kamar yadda Allah ya bani ita tafi yarana da suke manyan ina zan hada. " Idan ya zauna yana basu labarin yadda Aliyu ya saya mishi gida a sokoto, da yadda Aliyu ya mishi kaza, sai ka sha mamaki kamar ba Malam Aminu da aka sha dambe da shi ba. Rayuwa kenan a bangaren Inna kullum Addu'oin take Allah ya zauna da Yarta lafiya a gidan Mijinta. *** Kwara. Wani labarin da aka turowa Ummi shine, me yiwa a nime cutar da iyayen Sa'ade, domin ai izuwa yanzu Ummi hankalinta yayi nisa akan bankad'o abubuwan da ya faru shekarun baya. Domin ko sati Uku da ya wuce ta tura Ra'is Ka'inji dam. A can aka samo mata labari. Kallon juna suka yi da Ra'is. "Ummina, idan na fahimci wannan cases din Sultanate ce ummul'abasin? Kashe Sultan Abdulsamad ita ce da hannu a cikin sa." "Eh ta kashe Sultan Aliyu Dan Husaini sulu gambari, sannan a niyyar ta abawa danta sarautar, sai aka bawa Abdulsamad sarauta. Don haka idan tayi amfani da guba za ayi tunanin a cikin gidan nan ne, sai tayi amfani da sinadarin kulorin, wanda ya lalata huhunsa, haka ya sa ɓangarensa aka samu wanda yayi alƙawarin fansa. Shi kuma ya kashe Muhammad da Mahaifiyar sa. Duk saboda Sultanate kawai. Haka bai ishe ta ba, sai da aka kuma hada kai da ita domin kashe min Yarana. Duk da iya wannan shine hasashena." Shiru suka yi kafin Ra'is ya ce. "Amma kafin nan ba mamaki akwai wani abin da muka yi missing?" Kallon juna suka yi, kafin ya suka ce . "Tabbas mun yi missing wani abu!" ------ Shekaru hamsin baya. Sultanate ita ce Amaryan sarki ta biyu. Kafin ya auri wasu matan, uwar gidan ta Hajiya Saratu bata da tashin hankali ko ra'ayi akan mulki, sai dai mace ce da take da sani akan rayuwar mutane, wani abin sha'awa shi ne bata dauki duniya da fadi ba, kamar yadda Sultanate ta dauki duniya da zafi domin ita kamar Alfarma ce yasa take mu'amala da kananun mutane. Wannan yanayin yasa baki daya tafita daban, a bangaren mijin su. Baya jin dadin haka. Wani lokaci yana yawan musu magana su taya shi aiki da ta hanyar jan mutane jikinsu ta haaka ne zai fahimci Meye yake yi. Sai dai hakan bai samu ba ta wurin Ummu Mansurah sai ta Ummu Saratu, sun kai sama da shekaru goma kafin Allah ya azurta Ummu Saratu da haihuwar da namiji, sai dai yaron bai yi nisan kwana ba, ya mutu wanda Ummu ita ta saka aka bashi guba a cikin maganin daurinsa. Haka kuma Allah ya sakewa bawa Ummu Saratu wani haihuwar ta kashe jaririn, a na uku ne aka samu Abdulsamad. Wannan karon sai aka yi dace itama tana da cikin, amma tayi alwashin matukar ta haifi namiji sai ta kashe Abdulsamad. Sai dai Allah ya shirya mishi rayuwar sa da mutuwar sa babu wanda ya isa shirya ƙaddaran wani. A kwana a tashi har itama ta haihu, ta samu Abdurrhman. Haka yaran suka taso suna da shekara biyar Allah yayiwa Ummu Saratu rasuwa, daga Sultanate tayi da bawa sauran matan Sultan Aliyu guba don kar su dauki ciki, babu wanda ya sani sai gajiya domin da ita ake shirya kome. Sultanate tayi iya ƙoƙarin kafin ta samu ta kashe matan sarki daya bayan daya. Kuma har ya kai shi kansa sarki bata kyale shi ba, sai da ta kashe shi har lahira. Wani abin mamaki sam ba zaka dauka zata iya wannan aikin ba, domin fuskarta bai nuna tana kama da masu laifi ba. Haka Abdulrahman da Abdulsamad suka taso, idan da wuya tana kisa da Abdulsamad bai kai labari ba, Allah ya mishi yawan hakuri. Har suka ajiye mata, bai tab'a juyawa zancen Sultanate baya ba, bayan ta kashe Aliyu sulu gambari, tayi ta bada cin hanci a badawa Abdulrahman mulki aka ki shine aka bawa Abdulsamad, ko wata biyu bai yi ba, ta kashe shi. A lokacin babu wanda yasan wadannan al'amarin sai Hajiya Suhailah, ita kuma jin haushin abin da Sultanate tayi, shine ta jefa Muhammad dan wurin Yayar Badi'atul Noor a rijiya. Ya mutu, a lokacin Sultanate tayi mamakin haka. Sai aka yi rashin dace daga Sultanate har Hajiya Suhailah sunyi confront juna, wanda har Dawlat khatoon yayar Badi'atul Noor taji su, abin da ya haifar mata da nakuda kenan, Sultanate bata so a kashe Dawlat khatoon ba, amma sanin zata tona musu asiri yasa suka kashe ta har lahira. Ita da tagwayen cikin ta. Sannan suka hade kai wurin alkawarin ita Sultanate ta bawar Suhailah damar kashe duk wani Yaron da za a haifa a matsayin magajin masarautar, amma a bar mata Yaronta akan Mulkin da. Wannan shine mafi girman son kan da suka yi a tsakanin su, basu tab'a kawo Badi'atul Noor ita ce zata koma dakin yar uwarta, koda yake a bangaren su Badi'atul Noor akwai baffanta Badi'atul Noor kakan Latifah, mahaifin Hajiya Kudirat, wanda ta dauki yarda ta bashi, shi din yana da burin zama next King, sai dai tunda ya Tuntubi Mahaifin Badi'atul Noor, ya gaya mishi cewa yana son zama sarki ya ce mishi ko da wasa kada ya kuma maganar yana son mulkin domin surukunta ya hada su da sarakin.da yake kan mulki. Jin haushin haka yasa shi kashe Mahaifin Badi'atul Noor, sannan ya dauke hankalin kowa akan mutuwar, kana ya shiga jikin Badiatul Noor yana bada duk wani bayanin ta akan Ƴaranta.... (Lallai ma) #Mai_Dambu. [12/07, 9:09 am] usmanlauratu71: 63.... Ba iya Baffanta ba, mutane dayawa a cikin masarautar suna dakon ganin bayan Badi'atul Noor da yaranta, domin ko Hajiya Suhailah danta na biyu shi ya kashe Mansurah domin a lokacin yazo hutu. A daren da zasu kashe ta, don ta ji zasu kashe Abuturab ne a daren, koda suka kamata mahaifinta suka kira suka gaya mishi abin da ya faru, domin shima yana cikin masu son ganin bayan Ummi ai Ummi ba son shi take domin Allah ba, tunda Yaran da ta haifa da Abdulrahman na shi ne ta kai gidan Abdulrahman, sannan da ace da gaske tana sonsa tow kuwa da zasu kulla mummunar alaka a waje. Amma sai ta rike aurenta, akwai wasu yan siyasa guda biyu waɗanda wurin Sultan suka samu damar tsayawa a matakin jaha har zuwa kasa, sai gashi sune suka ɗauki nauyin kashe Saraki, Jalilah ita aka bawa gubar da tayi ta zubawa Maina yana ci a cikin abinci. Al'amarin ba iya nan ya tsaya ba, domin kuwa Sarkin kofa da ya shigo aka bashi aikin kashe jikan gajiya shima an sake bashi aikin ya san yadda zai kashe Abuturab amma yaki, domin sun fi hango nasara akan abuturab sama da su Maina, sai dai su din ana tunaninsu yana basu matukar aka kashe Yaran Sultan baki daya, bakin cikin haka zai kashe shi, no need ayi poisoning dinsa, sai dai kuma yadda Badi'atul Noor, ta katange kome yasa suka kasa samun nasarar kashe Abuturab. Amma tabbas sun so kashe abuturab.don har sokoto suka bi shi, basu same shi ba. Asalima sai Allah yayi ta nisanta shi da su, lokacin da aka kai mishi hari a london, Abdulkarim ne dan Hajiya Suhailah, wanda ya samu labarin sirrin fitar Abuturab ta bakin Latifah, itama abin da ya saka ta fada cikin shirinsu, domin tana kishin Mansurah tun suna yara, Abuturab baya kula su sai Mansurah kuma ai da banbanci basu gane ba ne, ita Mansurah tare suka tashi su kuma zuwa suke daga wata uwa duniya. Sosai makiya suka yiwa Badi'atul Noor kawanya musamman da na jikinta. *** Sanye suke da tafka-tafkan rigunan sanyi, a cikin jirgin kasar da zai kai su, Scotland domin ana tsannanin sanyi, kanta yana kafad'arshi, hannunsu sarkafe da juna. "Idan mu ka dawo za aikin ƙarshe, wanda daga shi nake fatar ki fara magana." Kara jingina kanta tayi a kafadar shi, ya rike yatsun hannunta da suke cikin safar hannu. "Ban san yadda zan miki bayanin yadda nake son ki ba, amma nasan ina son ki" tura baki tayi tana kallon shi domin kafin su fito yau, sai da Latifah ta mare ta, shi kuma ya rama mata. Hannu ta kai da zimmar tab'a fuskar ya rike hannun. "I'm sorry lucky!" Hawaye ne ya cika Idanunta. "I'm sorry kinji, haka ba zai kuma faruwa ba " gyada kai tayi tana share hawayen da yake zubo mata. Shafa fuskarta yayi yana faɗin. "Ba zata kuma dukanki ba, baki ga yadda kowa ya goyi bayanki ba, kiyi hakuri kin ji." Gyada kai tayi. Koda suka isa kai tsaye abin da ya kai shi, ya fara sannan ya kai ta masaukin da aka kama musu. Yawo tayi a cikin hotel din kafin ta koma dakin aka kawo mata abinci ta ci. Kunna tv tayi, ta jima kafin tayi sallah, bayan ta idar ta ci abinci sannan ta kwanta, karfe hudu ta tashi tayi wanka. Sannan ta sauya kaya, riga haf gown na Saint Laurent, cream cheese, hannun shi an saka mishi wani siririn net, gaban rigar a bude yake, iya cinya rigar ya tsaya sai Arab turba, wanda ake nad'e shi kamar dankwali amma hula ce, golden colour, tasan zuwa an jima zai shigo. Turaren da Ummi ta bata tun zuwan su, bata tab'a amfani da shi ba, shi ta dauka fa na kayan aurenta, tayi ta gogawa. Sannan ta dawo falon ta gyara ko ina, ta kuma gyara inda ta bata, ta zauna tana me daura kafa daya akan daya, tashi tayi ta je ta bude labulayen window, tana kallon yadda dusar ƙanƙara ya cike ko ina, tana tsaye taji an bude kofar, a hankali ta juya tana kallon shi, ware idanu tayi a kanta. Tun daga takalmin da ta saka, har zuwa saman cinyoyinta da suka bayyana kyan kayan a jikinta, total speechless. A hankali ya sake jakar hannunsa ya tako har inda take. Hannunsa ya kai habbatarta. Yana kallon jan bakin bakinta maroon colour. A hankali ya janyota jikin shi, ya rungume ta. "Irin wannan kwalliyar zai saka ni jin wani abu, na daban." Rufe fuskarta tayi tana dariya. "Muje ki raka ni nayi wanka." Bata so ba, amma haka ya biye mishi aka bata kwalliyar, tare da daura mata darasin shi ne ɗauka dogon lokaci a cikin kwakwalwar ta. Kafin suka fita, shiryiwa suka yi sallah magriba da isha, sannan ya nime abinci. Suka ci, daukar ta yayi suka fita bayan ta saka manyan kaya. Keke yaje ya ɗauka sai da suka fito gaban hotel ɗin, ya ce mata. "Hau muje yawo!" Baya ta wuce ya riko hannunta. "Nan zaki zauna" gabansa yake nufi, haka kuwa ta zauna suka cigaba da tafiya. Yana mata hira sai dariya take, har kusan karfe daya sannan suka dawo, ya mai da keken, juyawa yayi ya sunkuya tare da cewa. "Maza hau baya." Girgiza kai tayi tana dariya, sake mata magana yayi, ta kai hannunta bayan shi ta hau, ya kuwa zunkud'a ta. Suka fashe da dariya, haka suka isa har dakin su. Daga nan Abuturab ya daura mata karatunsa wanda yasan tabbas zai dauke ta shekaru kafin ya goge. Farko-farkon abin kuka take mishi, da tsoro amma yanzu sai gashi cikin ruwan sanyi har da kanta, take gayyatarsa wasu wuraren, idan har bai kai ziyara ba. Aliyu ya gama koya mata karatunsa me saukin ɗauka, saura babban karatun da ya rage a dauka, ya tanadi kome zuwa wannan ranar. Satin su biyu suka koma london, domin aikinta. Kwanan su biyar aka mata aikin, wuyarta zuwa bakinta, tsawon awa talatin da biyu aka dauka, sannan aka fito da ita. Magashiya. Abin ba karamin d'aga hankalin Abuturab yayi ba, domin gani yake kamar zata mutu ta bar shi, haka zuka cigaba da zaman jiran ta farfaɗo. *** Madina. Bayan fitowar Malam Aminu da abokin sa daga masallacin Annabi, zama yayi yana kallon shige da ficcen mutane domin malam Kalla ya ce zai tafi gida ba zai iya zaman sa'ido ba, kurawa wata mata idanu Malam Aminu yayi yana faɗin. "Wato duk inda aka hada mutane sai ka fahimci, Allah yayi halitta, yanzu ita wannan haka Allah ya yi ta, jibgi guda? Hodijam" ya fada yana kallon Yar Tunisia da take faman kokarin mikewa. Bai gama rufe baki ba, iyalinta suka tawo, suka taimaka mata ta mike, suna barin wurin shima ya mike. "Alqur'an dan dai kar a ce nayi son kai ne, ai bani ba komawa sokoto, ina dalili kome zaka ci kyau, ga madaran shanu ta gora, ga abinci da nama zuka zuka. Ai wallahi zan je na samu kalla mu zauna ko na wata shida ne mu nemi kudi " haka yayi ta tafiya har ya wuce masaukin su. Karshe dai malam Aminu b'ata yayi, kuma abin takaici har ta masaukin su yake wucewa niman gidan, sau uku yana wucewa karshe komawa masalaci yayi ya zauna, abin duniya ya dame shi ya ce. "Hmm ni fa wasa nake, babu wani zaman da zan yi a garin nan niman kudi, Ni Sokoto na zan koma don Allah don Annabi ku mai dani wurin Laminde na da Larai na." Ya fada yana fashewa da kuka, zama yayi yana sharban kuka. Suma a masaukin ganin bai dawo ba, yasa Malam Kalla komawa wurin su Inna ko ya dawo ya tsaya a wurin su ne, sai ya samu ai bai dawo ba. Babu shiri suka fito nimansa, tun daga can suka hango shi yana sharban kuka kamar karamin yaro. Takaici ya cika Inna Larai ta ce musu. "Kun gan shi can, yana tab'ara sai kace yaro kankana, mtseeeeeew Malam baka niman zamanin a al'amarin ka" "ikon Allah Malam Aminu!" "Wayyo Allah gyatuma ta, wayyo Allah uwata. " "Don Allah ka daina bawa kanka kunya, taso muje" Inna Laminde ta ce mishi. "Garin k'ak'a ka makale anan?" Share kwalla yayi ya ce musu. "Daga nace zan baka shawara, mu zauna a nan na wata shida tunda kome kyauta ne sai mu tara kudi, shi ne na manta hanyar gida!" Juyawa Inna Larai tayi cikin fada da sababi ta ce mishi. "da ace masu sace mutane na garin nan, sai na maka addu'a su yake kannka nan da bai da aikin sai lissafin dokin rano." Ta fada tana kwafa. "Larai kar ki manta, Arziki Y'ata kika zo ci ki daina min fada na gaya miki. " "An maka fada, idan dan kai ne bani biyo ka, na biyo ka ne don albarkacin Yaya da Sa'ade, wacce yar da ka nunawa duniya baka son ta." "Innalillahi, Laminde kin ji Larai zata min karya! Ni Larai zata dubi idanuna tace min bata ci arzikna ba? Lallai dole ki gaya min magana, kinci shinkafa da kaza, kin kora da madaran gora na shanu, kina baki a daki me raba dole ki gaya min magana " "Malam idan kai ne ka biya min aikin umran nan ka kore ni." "Don Allah Larai ya isa haka, haba don Allah dare ne fa." Inji Malam Musa kalla, "kyaleta ta dibe min albarka, bayan ta san muna garin Ma'aikin Allah, Kyaleta tsinuwar Mala'iku yayi aiki akanta, a toh mace ta lalace ta daidaice babu abinda ya sha kan Aminu, kuma Alqur'an baki kuma dangwalar arzikn Y'ata." Rigima sosai aka yi a tsakanin Malam Aminu da Inna Larai, ga abin dariya ga abin haushi, karshe cewa yayi wai tana mishi hassada don ba ita ta haifi Sa'ade ba, wannan kalaman ya bakanta mata rai, sai da tayi kuka, kuwa ai ta kullace shi a ranta, Washi gari suka wuce Makka, tunda suka isa Inna Laminde bata taɓa zama ba minti ɗaya don hutu ba, Addu'oin take wa Yaranta musamman yarta, domin kafin su taso na Nazifi ya bata waya sun yi magana da Abuturab akan ta saka su a cikin Addu'arta, aza ayi aikin karshe. Shi yasa ta kasa zama, koda suka isa Madina ma, Addu'oin ta sosai tai, sannan kafin su taso sun yi magana da Ummin itama ta roke ta da ta saka su addu'a, akwai babban al'amari da take son kawo karshen shi, shi yasa kome ta mikawa Allah. *** Kwara Anan kuwa kwara, saukar Alqur'an ake da sadaka, domin ummi tana son ta fitar da sakamakon binciken da ake nan da wasu kwanaki, domin nan da sati biyu Abuturab zai dawo, kuma akan zuwan shi zata fitar. Shi yasa baki daya, ake ta Addu'oin don al'amarin yazo da sauki, a bangaren Ra'is mahaifinsa zai iso tare da Abuturab. Part din Sultanate. "Likita baka ce kome ba, tun ɗazun kake kanta, kuma gashi zaka bar gidan." "Allah ya baka nasara, da sauki damuwa ce ta mata yawa, amma ba wani abin da yake damunta." "Tow shikenan" ya fada yana kallon Sultanate da take barcin allura. Domin kwana biyu nan, ita tasan.me take, jikinta kamar ana konata ta cikinta, gashi tana shan ruwa kamar me, haka kuma bata isa ta kwanta ko ta rufe Idanunta ba, Dawlat khatoon zata gani a tsaye a gabanta cikin jini. Firgi zata bude idanunta. abinda ya haifar da haka, saukar da ake da yankan da ake yi, shi yake karya duk wani asirin da aka yi domin rufe bakin mutane da jama'ar masarautar baki daya. Tow addu'ar da ake bata faduwa banza, domin kuwa ya fara bankad'o abubuwan da yawa, a gefen Abdulkarim, wanda ya kashe Mansurah bayan ya mata fyade, kama shi hukumar Saudiya tayi dama duk abin da Hajiya Suhailah tayi domin shi take, tow gashi ya tab'o me tsada a Saudiya har an kama shi.. *** UK.... #Mai_Dambu [13/07, 10:03 am] usmanlauratu71: 64... UK. Rike hannunsa tayi tana kallon waje, kafin sauke ajiyar zuciya. Duk da an mata aikin bakin ko zata yi magana, amma har yau shiru babu alamar zata yi magana, idanunta ne ya cika da kwalla. Daga yadda ta razana ya sa shi fahimtar akwai wani abu a ƙasa. "Meke faruwa?" Hawaye ne suka zubo daga idanun ta." Ta girgiza mishi kai tana. "Gaya min wani abu na faruwa ne?" Hawaye ne sharr suka kara zubo mata. Da hannu ta mishi magana ta ce. "Kar ka fita zata zo!" Murmushi yayi sannan ya saka hannu ya rungume ta. "babu abin da zata iya miki, matukar ina raye.!" Ya fadi haka tare da barin ta a wurin ya shiga hada kayanta, domin an sallame ta. Sai da ya gama kome sannan ya fita da kayan da ita suka fita tare ne, bai san me Latifah take bukata ba. Saka yayi a mota, sannan ya koma cikin asibitin. A kofar dakin ya hango ta da yar askar da aje tiyata, tsayawa yayi ya ga ta shiga cikin dakin. Rufa mata baya yayi ya rufe kofar a razane ta juya, domin bata kawo ya fita da Sa'ade ba. Sake askar tayi. "Kakanki ya saka miki mummunar ciwon da ba zaki tab'a warkewa ba, da ace haukar ki ya kai matakin da kika tab'a min yarinyar da nake Bala'in so da kin sha mamaki, ban san me kike so ba, ni dai na ce bana sonki kuma na kara gaya miki bana sonki, wace ce ke da zakina bibiyar matata? Tunda abin ya kai ga haka zan hada ki da hukuma, kuma karshe sai kin rasa aikin ki!" Zubewa tayi akan gwiwanta tana me fashewa da kuka. "Don Allah ka rufa min asiri, wallahi ba zan kuma tab'a ta ba, don Allah." "In one condition, matukar kika shiga harkokin ta, wallahi sai na gayawa Mahaifinki abin da kika aikata " daga haka ya juya abin sa, matukar abuturab ba autar maza ba ne, ta hakura da shi, amma kuma ina zata samu namijin da ya iya sarrafa mace ba tare da ya kai last stage ba. Yana fita wurin motar ya same ta sai zare idanu take, murmushi jibi zasu bar london ya gama kome na shi domin ita, zai karasa sauran a lagos. Kusan satin ta huɗu a asibitin, koda suka isa a tare suka shiga kitchen, sumbatar wuyarta yayi, suna aikin karshe da suka kusan gamawa ne, ya dauki garin fulawa ya bata mata fuska da shi, ware idanu tayi, ta dauki sauran fulawan ta shafa mishi a jiki ta fita da gudu, ya bi bayanta, suka shiga zaga falon, kamar zasu tashi gidan da dariyar su. Kamota yayi ya mannata da bango, sosai yake tura mata sako masu saukin ɗauka, yana ji wani irin Kaunarta zuciyar shi tana kara narkewa akanta. Definitely ya gama mutuwa akan yarinyan nan, lokaci kadan yake jira su zama daya. Daukarta yayi zuwa cikin bedroom dinsu, wanka suka yi a tare, sannan suka fito. Mini skirt na jeans ta saka, sai hafvest da ta daura pink, gashin kanta ta daura shi bayan ya busar mata da shi. Komawa ban daki tayi, jin shiru shiru yasa shi fahimtar tutu take, toroso. Fita yayi daga dakin, tana gamawa ta kuma gyara ban dakin ta fito. Sai da ya shafe jikinta da turare, sannan ta futo wurin cikin abincin. A tare suka ci abincin, sannan ta tattara kome ya fito musu da popcorn, suna kallo suna ci, har Azhar, a tare suka nufi dakinsu, suka yi alola ya ja su sallah, suna idarwa suka shiga hada kayan su. A hankali suna yi yana mata hira, murmushi kawai take, kafin la'asar sun gama hada kome, sallah suka yi, suka shiga hada ba wajen, suna tsokanar juna, wunin ranar tattara kayan su, suke. The next day suka tashi da aikin cire kome a gidan suna sakawa a kwali, domin ya ce ba zai kuma dawowa london ba. Haka suka yi ta sakawa a kwali ana rufe bakinsa, wurin sha biyun rana babbar motar dauke da kwantena tazo ta kwashe kayan. Da kawun sa ya haɗa a waje. "Kana ta shiri kenan?" "Eh Uncle in sha Allah zan tafi gobe." "Allah ya tsare hanya" "Amin Ya Allah" ya fada yana tsaye suna ta zuba mishi kayan a motar, har suka gama sannan yayi cike ciken da zai yi suka tafi shi kuma ya koma cikin gidan, tana kitchen, wando ne a jikinta irin crazy din nan, sai bodyhook, a hankali ya isa bayan ta, sumbatar wuyarta yayi yana faɗin. "Kina kunna min wuta fa" murmushi tayi hannun shi ya kai cinyarta yana shafawa a hankali. "Idan kina irin wannan dress din, zaki hana ni, abin kirki domin nayi ta tunanin wadannan halittun." Juyawa tayi tana kallon shi, sumbatar bakin shi tayi, ya riko ta tsam. Sun kwashi mintina goma sha a haka, don ma Allah ya taimaka abin da ta daura bai zube ba. Dakyar suka yiwa juna a falon, kamar cin wuta haka suke biyar da kansu. Turo kofar falon Latifah tayi, ta hango yadda suke wani abu. Da sauri ta mai da kofar ta rufe, tayiwa kanta alkawarin bata kuma shiga rayuwar su, amma a duk lokacin da ta gansu a wannan yanayin ji take kamar ba zata iya ba. Su kan can suka lula, sai dai yau Abuturab yaso wucewa, ganin yadda jikinta ya dauki rawa da tsoro ya sa shi dole ya kyaleta. Ya koma gefe, yana me rungume ta. "Sorry " ya fada a hankali, domin gaskiya yasan yana kwaruwa, shi yasa yayiwa kansa alƙawarin suna isa kwara, wallahi hakurin sa ya ƙare. Haka suka shiga wanka a tare, koda suka fito sallah suka yi, da yamma suka fita yawo tare da tsaraba, haka tayi ta jidar turare da kimono wa Ummi da wani arab shop ta sayawa Rumaisah da Zakiyyah da Ummy Aymana dogayen riguna, duk da shi ya bata kuɗin, Innar ta da yayunta, atamfar Super exclusive ta sayawa Inna kala biyu, sai Inna Larai ba, Abuturab ya karawa Inna lace mai kyau, sak irin na Inna, sannan ya kaita inda ya sayi kimono yayi ta saya mata, me hade da riga da wando, ko riga da skirt. Takalma kuwa haka yayi ta jida mata. Sannan ya sayawa Malam Aminu shadda me kyau da tsada. Wani gefe suka shiga yaga wani rigar barci lingeria, ya ɗauka yana son first night dinsa da ita shi zata saka, janya yayi suka tafi suka biya kudin kayan, sannan suka bar kasuwar. Koda suka dawo kayan ya zuba a cikin akwatin da ya sayo, bayan sun kwanta yana cikin jikinsa ya ce mata. "Ki shirya domin wallahi bani d'aga miki kafa."kifa kanta tayi a kirjinsa tana dariya. Ba zata tab'a manta da wannan moment din ba, yana cikin ranta da brain ta ba. Washi gari, da asuba cab yazo ya dauke su. Suka bar Ingila, akan idanun Latifah suka bar gidan. Basu samu jirgin Lagos ba, sai dai sun samu wanda zai isa dubai,kafin su samu na Lagos. Tafiyar kwana ɗaya da wuni daya. Suka iso Lagos a gaji suka samu jirgin kwara. Koda suka iso kwara, Ra'is ya je ya dauko su. Sun gaji musamman ita, suna isa bangaren Ummi suka sauka, anan suka ci abinci suka huta. Da gayya Ummi ta dauke ta, shi kuma ya nufi cikin gidan gaida mutane. Ko ba a gaya maka ba, kasan ya samu nutsuwa a auren da yayi, don haka kowa ya gansa sai ya yi magana akan kibar sa. A bangaren Sultanate ya yada zango. "Munafuki me ya dawo da kai?" "Nazo binne ki da ranki ne, sharrin da kika yi su raka ki har makwancinki" yana fadar haka ya bar ta, sallah magariba aka kira ya nufi masallaci, bai dawo ga sai da aka yi sallah isha. Sannan ya dawo ya nufi bangaren Ummi abinci ya ci, kiri-kiri ya saka Sa'adensa a gaba, haka kawai a hana shi matarsa, tun fitarsa Ummi ma gyara mishi matar take, bawai ta rike ba ne. Suna shiga part ɗinsa wanka yayi sannan ya dauko mata doguwar riga da a cikin kayan sa, ta bata ta sauya kaya, alola tayi suka gabatar da sallah nafilla da ma'aurata suke yi a daren su na farko. Bayan sun idar, ya fita ya kawo musu, fita yayi sai gashi dauke da hollandia milk, ya ajiye cup biyu, ya zuba mata daya shima ya zuba daya suka sha. Yana jan ta da hira. A hankali ya dauki kofin ya fita da shi ya dawo, brush yayi itama kuma tayi, kafin ta fito ya ajiye mata rigar barcin. Tana fitowa ta samu baya dakin, daukar kayan tayi ta shige ban daki, ta saka sannan ta fito ta kwanta. Kamar ya sanin ta gama kome ya shigo shima, tunda ya haura gadon, yake kashe ta da al'amarin soyayyarsa, wanda ita kanta ta saba ba wani sabon abu bane, sai dai kuma labarin ya sauya ne a lokacin da ya isa matakin farko ta nasarar zaman su abu daya, lallai ana sha gwagwarmayar a wannan fagen, domin kuwa ita kanta da tasan haka abin yake, da koda wasa ba zata yarda ta bashi yarda da amanar ta ba, domin sai da ya gwangwaje amarcinsa, ya kai matakin da ba zai iya hana kansa gamsuwa ba, ya kyaleta. Ina dalili, shekara nawa yana dakon zama magidanci yanzu da ya samu babu me hana shi, ban daki ya shiga ya gyara jikinsa, sannan ya haɗa mata ruwan zafi, da kansa ya taimaka mata, ya kwashe zanin gadon, ya ajiye. Domin Ummi ta bukaci haka. Lokacin da ya fito da ita daga ban daki, kuka take da rigima dakyar ya lallabata suka kwana, cikin dare zazzaɓi ya rufe ta, haka ya kwana yana rarrashinta, ga shegen raki. Asubar farko ya bugawa Ummi kofa, tana zauna akan abin sallah, ya shigo dakin. Sunkuyar da kai yayi a gabanta. "Na gode da kika bani duk wani tarbiyyar da ta dace, Ummi na gode da taimakon da kika min na zama D'a nagari, Ummi ki saka idanu a kaina da iyalina koda zan kauce hanya" "Allah ya maka albarka, ya Fulaninta take " sunkuyar da kai yayi ya ce. "zan tafi masallaci, ban san me zaku bukata ba" "ka koma gidan su Ra'is zamu kira ka idan muka bukaci wani abu " haka ya mike cike da kunya, a lokacin ta mike tare da nufar wardrobe dinta, ta dauko sabuwar alkyabarta, sannan ta dauki da wasu awarwaro na gold da dan kunne da sarkan su, har da sarkan kafa da bariman hanci, wani shegen lace ne na alfarma ta fito da shi, waya ta dauka ta kira Zuwairah. Can kuwa sai gata a tare dq suka nufi part din Abuturab. Kaya sosai Ummi ta shiga da shi, sai da suka shiga uwar dakin ta hangota cikin bargo a dunkule, nan Ummi tayi ta shafa kanta, har ta bude idanunta, fuskar ta tayi jajjur, sai kuma.ta fashe da kuka. Haka Zuwairah ta hada mata ruwan zafi, ta saka duk abin da ake bukata, sannan Zuwairah ta basu wuri Ummi da kanta, ta rikota tare da mika mata towel, ta taimaka mata har zuwa ban daki, yadda take tafiya sai ta baka tausayi domin baki daya tayi laushi. Haka dai Ummi tayi ta mata bayani, har ta gyara jikinta, sannan ta fito, kiran Zuwairah tayi ta tsaya ta shirya suka wuce ɓangaren Ummin, dauke da zanin gadon da suka yi tarzoma akan sa, aka saka a tire, ana bin part part na gidan nuna musu abin da ya faru daren jiya, don haka duk matar da aka kai.mata, haka zata cire gold ko kudi me yawa ta fanshi zanin gadon da gadon da suka kwana, har wurin Sultanate aka kai, ta fanshi gadon Zuwairah ta ce mata. "baku fansa yadda Umminsa ta fansa ba, ta fansa da gwala-gwalan tire daya, sai kudi miliyan biyu, da mota Land cruise, sai kujeran hajji, da yawon buɗe ido, ku kuma.baku fansa yadda ya da ce ba. Don haka yau akwai walima." [13/07, 10:03 am] usmanlauratu71: 65... Sosai Sultanate ta kadu, duk da halin da take ciki bai hanata balai ba, amma kuma ciwon da take fama da shi ya ishe ta. Zuwairah sun bar gidan suka tafi bangaren Ummi, kafin kace me yayun Abuturab sun zo suma.sun fanshi zanin gadon, amma ina Ummi ta jima da musu kane-kane akan Ƴaranta, zuwa rana gidan ya cika, zazzabin da ya rufe Sa'ade yasa dole aka d'aga walimar, amma fa anyi karamin biki ko.nace ana kan biki a cikin gidan. Sai dare suka samu zazzabin ya sauka, domin sai da aka saka mata ruwa, a lokacin Abuturab ya zo har dakin Ummin da take kwance, ya shiga. Zama yayi a gefen gadon, yana shafa fuskarta. Bude idanu tayi tana kallon shi, kafin ta dauke kai domin fushi take da shi, "kiyi hakuri" ya fada yana ciro wani karamin box ya ciro mata wani sarkan diamond ya saka mata, sannan ya saka mata zoben, yana mirza hannun. "My love for you is deeper than the deepest ocean taller than the tallest mountain hotter than the hottest desert and denser than the densest of forests my love for you is truly eternal I love you." Ya fada mata, hawaye ne ya zubo mata. Yana share hawayen ya cigaba da cewa. "Behind every successful man is a woman ? Whoever said this is 100 percent right. You're the secret behind my success, my dear wife. I love you. ina son ki, ina son ki, zan kuma cigaba da son har numfashina a karshe. Nasan wata rana zan saka ki a cikin damuwa ki min uzuri da kawaici ni ma dan adam ne, zan iya laifi a koda yaushe. Ina son ki lucky." Ya ciro sabon waya ya daura mata a kan hannunta. "Idan na koma zan kira ki Please kar ki kashe wayar, ina sonki" ya sumbaci goshinta, sannan ya mata sai da safe. Ummi tana bakin kofar, tausayi ya bata domin da gasken gaske son Sa'a yake kuma irin mahaukaciyar soyayya ce mara jin rarrashi. Lokacin da ta shiga dakin tana ganin yadda take kokarin boye wayar, sharewa Ummi tayi, irin bata san kome ba, sannan ta shiga ban daki ta hada mata ruwan zafi, ta taimaka mata ta shiga ban daki tayi wanka, tana fitowa ta samu ta ajiye mata tea me zafi da farfesun kazar gida. A hankali take shiryawa, tana gamawa ta fara sha, tana lumshe idanun ta. Sai dai har lokacin bakinta babu dad'i ko.kadan. Tea ɗin ne ta ji daɗin, kara wayar ta ji ta bude. ```The best day in my life was the day I married you the best thing in my life is you I cannot imagine a single day without you i've said it once, and i'll say it again I love you!!``` murmushi tayi tana jin saukar kalamansa kamar yadda sanyi yake sauka idan babu riga a jikinka, seriously wani bala'in kaunarsa take ji. *Love ... I want to hold you close to me and feel our hearts beat as one … forever ....* ta tura mishi, kashe wutar dakin Ummi tayi, sannan ta fita, ai kamar an basu damar amayar da abin da yake cikin ransu ne. A hankali abubuwan masu yawan gaske suka yi ta kankama a cikin daren nan, soyayyar junan su da suka gaza boyewa. Sai wurin Biyu na dare ta kwanta, Washi gari aka tashi da gaggaumin walima, wayyo Allah. Biki aka yi sosai, kafin zuwa dare an watse aka mai da amarya bangaren. Tunda ya sha ruwa kafin ya fita sallah isha, yake jin kamar ana rike mishi numfashinsa dakyar aka kai raka'ar karshe ya yanki jiki ya fadi yana aman jini. Rungumar shi Ra'is yayi."Abuturab!" Ya fada da ƙarfi dan dole domin sallah da aka yi sallamar shi a gaggauce aka tafi asibiti da shi, kafin kace me labari ya bazu a gidan Abuturab ya faɗa, dole aka yi arrested din duk wani Maid na ɓangaren Ummi domin daga ɓangaren ya wuce masalaci. Ita kanta Ummin asibiti suka nufa da Sa'ade da take kuka sosai, gashi da kyar take takawa, a asibitin suka kwana, Dole Washi gari aka tura su Abuja, jikin Sa'ade yayi sanyi sai kuka take, akwai gidan Sultan anan Abujan anan suka sauka. A can kuwa kwara bincike da yayi bincike ga azaba, dole yasa Jalilah fadar gaskiya ita ta saka mishi guba, domin tace zata fadi gaskiya ne a gaban Sultan domin yace ba zai tafi ba, Ra'is da Ummin. "Waye ya baki guba kika saka mishi.?" "Sarkin Malamai, Alhaji Sani, sai Sultanate, da Hajiya Suhailah, da Dauda Jama'a, da Sanata TJ, Dr Muhammad Ismail, sune suka biya domin sun tabbatar Aliyu zai gaje ka, a hannun shi na karbi kwangilar kashe Maina da Saraki, nice ba taka kan Saraki, nice na kashe Gajiya da jikanta, naso kashe Ummi ammada zaran ka kusancin inda take, ba zaka iya mata kome ba, domin akwai wasu irin mutane da suke kare ta, nice nayi ta bibiyar Aliyu tun yana matashi ina cutar da shi, domin Ummi ta yarda da ni, nice na kai musu hari lokacin da ya kwana gidan Ummyn Aymana." "Duk saboda me kika yi haka!" Dariya tayi sannan ta ce mishi. "Saboda ina sonka Sultan, idan na kashe yaran Ummi da ita shi ne Sultanate zata saka ma aure ni kuma na haifa yarimomin gobe , ai an bani guba na saka maka,amma Zuwairah ta tura sakon har zuwa wurin Ummi, karshe sakon ya fada hannu, na cewa Zuwairah matukar ta tona min asiri, sai na kashe D'anta." Magana marasa dadi, haka tayi ta fada. "Daga baya na fahimci karfin Ummi shi ne Abuturab, shi yasa na saka mishi guba ana bikin zaman shi cikakken ango, yayi murnan a lahira itama matar sa sai na kashe ta babu me kara haihuwar da namiji. Domin na fahimci ummi ko Badi'atul tafi kowacce mace daraja a cikin gidan nan, kamar yadda Uwata ta kare rayuwarta, tana bauta mata haka take son na kare rayuwata ina bauta mata, bayan nasha bibiyar rayuwar auren ku, ina ganin yadda kake haukata ta, tana kuka tana ihu so nake naji haka, sai akayi dacen muradun sauran mutanen yayi daidai da nawa." Shiru tayi kafin ta kwashe da dariya. "Kujeran da kake kai, da jinin matar ka, Dawlat khatoon da Danka Muhammad aka samar maka, sai da aka zuba da jinin mutanen da babu ruwan su, ka tambayi Sultanate, jinin mahaifinka, Jinin Dan uwanka Abdulsamad, jinin matar ka da jinin Yaran ka Maina da saraki, sai.jinin Mansurah domin taji kome, Ubanta Marwan yana jin haushin ka, ya sadaukarwa da yarsa, me kake son sani?". ".ku tafi da ita, sannan duk masu hannu a zakulo su, ita kuma ku b'atar da ita, yadda ba a kuma jin labarin ta ba, idan da hali mazan ma kusan yadda zaku yi da su. Sauran xan ji da su, wannan umarnina ne na bada. Kafin Aliyu ya dawo ina son a share min kowacce kazamta, Suhailah da Sultanate a kyale su." "An gama Sultan " Kamar yadda ha bada umurnin haka, aka yi ta bin daya biyu ana kama su, tare da tattara su, har lagos. Babu abin da ya fi ciwo a dauke ka a tafi da kai duniyar da baka sani ba, a cikin kwantena aka saka su, Dan majalisar wakilai da na dokokin kasa, sai baffan Ummi, aka dura su a cikin kwantenan, sannan aka saka su a can ƙasar kwantanonin, aka share su da sunan za a kai kaya zuwa China ne. ** Har dakin Sultanate Sultan ya shiga tana kwance. "me yasa kika sadaukar min da jinin Iyalina? Me yasa jinin Yarana da Matata? Kina haka ne don kar mulkin ya fita hannuna? Umma kin yi kuskure, Aliyu shi zai cigaba da da mulki uwarsa tana gefensa." Yayi magana me zafi, yana kuka kafin ya mike ya fita, wata rayuwar tana bukatar sadaukarwa. Dole ya hakura da kome. Yana fita daga cikin part dinsa, aka rataya mishi igiya, duk yadda yaso ya kwaci kansa, haka suka sakale shi. Suna gama fahimtar ya tashi aiki, jami'an tsaron masarautar suna musu kawanya, tare da haska su, Hajiya Suhailah da Dan uwanta. Kama su akayi, shi kuma Sultan Abdulrahman ya rasu, dama duk rigimar domin shi ne. Kafin kace me labarin ya cika masarautar. *** Tunda ya farka yake rike da hannun ta, yana faɗin."Ummina ki min addu'a!" Ya fada cikin matsanancin azaba, hawaye na zuba mata ta ce mishi. "Abu Turab naga gawar Abubakar ban yi kuka ba, na ga gawar Umar ban yi kuka ba, Abu turab me yasa nake kuka akan ka? Me yasa nake kuka? Me yasa na rasa kwarin akan ka" fitar da ita nurse suka yi, tana ta kuka. Sa'ade kan, kira tayi daga Sokoto yau da safe aka da Inna suka tafi da ita, domin itama birkicewa tayi bata da lafiya. Babban tashin hankali shi ne dashen huhu za a mishi. Lokacin da za a tafi da Sa'ade, Abdulhakim shima yazo asibitin domin ciwon sa ya ci karfin shi, don haka yazo ganin likita ne yadda yadda ake rike-rike tsakanin Ummi da Sa'ade ba zata tafi ba. Tsayawa yayi ya ga har an saka ta a mota tana ihu. Shiga asibitin yayi ya ga likitansa, sannan ya nime jin matsalar Abuturab. "Ana niman huhun da za a saka mishi nan da awa ashirin da daya, idan babu zai daina jan numfashi ne karshe kuma kasan mutuwa ce!" "Tow ni saura kaso nawa na tsammanin zan rayu?" Bude takardan likitan yayi, ya ce mishi. "Ai kai Ikon Allah yake tare da kai, domin babu wani hope sai na kudirar Allah" murmushi yayi sannan ya ce. "Allah ya jinkirta min mutuwa ne, domin nayi aikin alkhairi, idan aka.cire nawa shi zai tashi!?" "What baka da hankali ne?" "Eh gaskiya bani da shi, a cire min nawa a saka mishi, albarkacin Sa'adatu,ina son ta amma ba zan tab'a ganin tana kuka akan abin da take ba, zan gayawa Iyayena ayi aikin kawai." Kafin kace me Abdul ya kira mahaifinsa ya gaya mishi, ya kuma kira Mahaifiyar sa, ya gaya mata. Domin da farko taki ya ce ko taso ko kar ta so mutuwa zai yi, gara abawa mabukata akan ya tafi haka. Kafin zuwa dare iyayen shi sun iso,yadda yake bayyana musu soyayyar Sa'adatu yasa basu ja ba, koda suka nufi Ummi da al'amarin,shiru tayi ta share hawayenta ta ce mishi. "Abdulhakim,kana da rayuwa bamu san me Allah ya hukunta ba, ka je kayi rayuwarka,ka bar shi idan Allah ya nufa zai tashi shi kenan" "a'a ni na yi niyya, mutuwa xan yi, shima kuma haka.kike son ya mutu? Waye zai saka Sa'ade a farincikin? Tunda ina da damar saka su su rayu dukkan su biyu a cire mishi suyi farincikin rayuwa kawai." Sai da Hajiya Daula ta saka baki, Ummi ta yarda, aka yi aikin, da ya dauki kwana guda ana abu daya, wani ikon Allah ana cire huhun Abdul aka yi wani hatsari, gayen ya mutu ba asan kowa na shi va, likitan Abdul ya nime izinin cire zuciyar gayen aka bashi domin shima ya rasu akan lokaci aka cire zuciyar shi da Huhun aka mai dawa Abdul tare da dashen zuciyar shi, Ko Allah zai saka ya rayu. Haja dukkan su aka turo su. A lokacin likitan ya tara su ya musu bayani, "Allah yana taimakawa masu taimakon al'umma ba tare da sun nime wani abu ba, irin fafutukar da yayi domin ya rayu shi ne naga gara a maida mishi organ dinsa da kuma sabon zuciya, Abdulhakim ua haifu domin ya hakura da farincikin sa yarinyar da yake so ta rayu, bai yi tunanin ya rayu koda wancan mutu ya same ta ba, burin sa suyi farincikin, nima kuma na bashi kwarin gwiwa ya rayu ya taya su farinciki yana da tashi rayuwar shi yasa har Allah ya kawo wancan mamacin domin dukkan su, su rayu shi ne Allah ya dauke rayuwar wancan mamacin Tsarki ya tabbata ga makagin halittun farko da na karshe ........ Shin Allah mun kusan kwashe shirgin mu🙄🤣 [14/07, 9:42 am] usmanlauratu71: 66..... Sosai maganar likitan ya kashewa Ummi jiki, koda yake shi Allah haka yake al'amarinsa. Suna cikin tattaunawar Ra'is ya shigo tare da mahaifinsa. "Sultanah Kwara fa tana ci da wuta!" D'ago kai tayi tana nazarin maganar kafin ta ce. "Ba maza ne a can?" Girgiza kai yayi cikin jimami ya ce mata. "Maza sun fadi." Mikewa tayi, a hankali tare da buga Kirjinta. "Maza sun fadi?" "Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari ya fadi?" Sunkuyar da kai yayi cikin damuwa, "Ra'is ka zauna da Abuturab muje" "Sultanah ai mun zo da jami'an tsaro zasu kula da lafiyar shi, domin sarki ne me jiran gado." Juyawa tayi cikin dauriya kamar zata fasa ihu ta cewa Likitan da su Hajiya Daulah. "Kuyi hakuri mijina kuma sarkin kwara ya rasu ba zan iya zama a nan ba." Gyada kai suka yi tare da mata ta'aziya. Kafin kace me asibitin har ya samu halartar yan jaridu, domin kuwa dayawan su, sun ji labarin rasuwar Sarkin kwara, sannan sun ji labari. Ai anyi dashen huhu a asibitin al'amarin sai ya zama babban al'amari. A private jet suka nufi kwara, kafin su isa manyan mutane da sarakunan daular Uthmaniya sun cika garin. Anyi sallah jana'izar karfe biyu na rana Alhamis. Ummi taci kuka sosai domin ba zaka gane lokacin da tayi kukan ba, sai dare da ta kwanta a lokacin ta nime kowa ya fita mata a daki, a sannan tayi kuka kamar me, tasan iyayenta ta zauna da su, tsawon shekaru sha shida amma sultan ta zauna da zauna na tsawon shekaru arba'in da tara, a wurin shi ta kare yarantarta. Yau kuma a ce babu shi. A bangaren Sultanate kuwa hauka ce bata yi ba, sai dai ta kullace mutane dayawa a ranta domin gani take kamar da gayya Badi'atul Noor ta kashe mata shi. Bayan kuwa tasan ba ita ba ce. Sai da aka yi addu'ar uku sannan, aka fara maganar gaskiya, a lokacin Wazir Dawood ya bayyana kansa, abin ya bawa kowa mamaki, domin koda aka tambaye shi hujjar boye kansa, nan ya shiga basu labarin binciken da yake da barazanar mutuwar da aka masa, sannan ya ce musu. "Zan fita daga ɓangaren Sultanate na hadu da Abdulkarim, yadda ya min ya sani fahimtar zai kashe ni, shi yasa ko da na fito bangaren sai na wuce bangaren Badi'atul Noor, ana na shiga motar Rumaisah aka fitar da ni, nawa motar kuma aka kunnata aka saka karfe a jikin birkin aka fitar da ita daga masarautar. " "Allah ya tsare na gaba, ina Abdulkarim din yake yanzu?" Inji Galadima. "Saudiyya ta kama shi da laifin safara da miyagun kwayoyi, kusan hukuncin kisa ce a can, a nan kuma zan iya cewa za ayi kuri'a ga masu ra'ayin shiga takarar neman kujerar sarautar masarautar nan sai su yi magana, amma ni ina tare da Abuturab ne!" Shiru kowa yayi sannan sauran emirate council suka ce. "Ko akwai me ra'ayin kujeran?" "Babu gaskiya nima ina bayan Abuturab!" Kafin wani lokaci, sun bada goyon bayansu, tare da cewa zasu Yi aiki da shi bilhakki da gaskiya. *** Sokoto. Rikice musu Sa'adatu tayi, har da zazzaɓin ta, ana cikin fama da ita ne, aka kira Allah yayiwa surukinta rasu, don ko da aka ce surukinta ya rasu, suma tayi domin gani take boye mata aka yi, bayan tafiyar su Sadeeq, ne Ummu Hafsah tayi ta rarrashinta, amma fir taki shiru dole sai da aka dauko Inna Laminde da suka dawo Umra, ita ta kai ta Maikulki, a can ne suka samu kanta, amma rigima da wanda ya kai kuka da wanda bai kai kuka ba, tow sunan su kuka ne. Tattara shirginta Inna tayi ta watsar, ta cigaba da harkan gabanta. Karshe da ta ishe ta, ta rufe da fada tana cewa. "Na rantse da Allah kika ishe ni sai kin koma can gidanki, domin wallahi ban ciki da rashin mutunci." "A dai tausaya mata, bana son tashin hankali, yarinyar tana cikin damuwa a kara mata da wani." Inji Malam Aminu, domin a duniya ya tsani wanda zai batawa Sa'adatu rai. Tsaki Inna tayi, bata kula shi ba. *** Bayan sati biyu da musu aiki, Abdul kullum yana wurin Abuturab. Wadanda suka zama kamar abokai, wani abun alkhairin shi ne yadda suka manta da Sa'ade a tsakaninsu. Suka rungume kansu a matsayin musulmai dan uwan Muslim ne, haka ba karamin dadi yayi ba, shi kan Abdul imagine yake da yau gashi ga sarki, domin abin da ban mamaki, yadda rayuwar Abuturab din yake gudar dashi babu mulki babu izza, nutsuwa da mutumtaka. Sannan yadda yake waya da mutane. Musamman Mahaifiyarsa. Cikin girmamawa, tare da bata dukkansa. Shigowar likita yasa shi ajiye wayar da yake. "Dr ina son zuwa ga matata amma baka bani damar haka ba, haka zan ta zama?" "Your highness, muna kokarin ganin mun duba lafiyar ka ne sama da kome." Dariya Abdul yayi ya ce mishi. "Kasan dai ni surukinka ne domin Yayan Sa'ade nake, kana jin kunya ta mana!" Murmushin gefen baki yayi, ya ce mishi. " Tow zan duba yiwuwar na ji kunyar ka." Haka suka yi ta hira. Har likitan ya gama duba shi, ya duba Abdul ya ce musu. "nan da kwana uku zaku tafi!" "Harararsa Abuturab yayi ya ce mata. "I can't wait har kwana uku!" "Idan kaso sai ka tafi ai" dafe kansa yayi ya ce. "ka rena mana sarki fa Ra'is!" Tsaki Ra'is yayi ya ce mishi. "Waye Sarkin? Wannan dan iskan? Tir da samun banzan sarki irinsa " "ka iya bakin ka,domin sai mu hana ka shiga kwara." Abdul ya fada yana dariya, kiran Nazifi yayi ya gaya mishi cewa yana zuwa nan sokoto a tabbatar an kintsa gidansa na Maikulki, ya amsa mishi da tow. - Yau Asabar, tana daki kwance. Ta ji muryan Inna Laminde tana faɗin. "Sannu ku da zuwa sannunku" ta shigo daki ta dauki taburma tana faɗin. "Auta fito ga baki nan Kinyi" fitowa tayi tana sake baki, Rahilah da Husnah, da wani irin gudu suka rungume juna, suka kuma shige daki sai kuka da farincikin. Nan dai suka sha kukansu, sannan suka buge da hirar su. Suna cikin hiran Nazifi yazo da sakon Abuturab. Ai kuwa babu shiri su Inna suka tisa keyarta rakiyar Inna Larai, suka tafi gidanta. Ga kayan abinci da Nazif ya kawo. Don haka suka shiga aikin gyara kome har da Inna Larai, suna yi suna taɓa hira, abinci suka yi dake akwai kayan lambu har gidan Mai gari, aka kai. Inna Larai ta wuce da nasu, ita da kawayenta suka naje a falo ana hira. Bayan sun ci abinci sun huta suka shiga zaga cikin gidan. Anan suka ga hoton su. "Dama shi kuma aura?" Murmusawa tayi ta ce musu. "eh shi ne!" "Ina wancan mijin da aka ce kin kashe?" "Yana raye rabuwa muka yi!" "Allah Sarki." Nan suka dawo falo suka baje. Kafin suka kalli lokacin. "Zamu koma gidan Inna mu kwana sai jibi da safe zamu koma." "A'a ga part dina." "Idan mijin ki baya son baki fa?" Hararan su tayi tana faɗin. "Shi din Yarima ne, kin ga babu yadda zai ki baki " a kofar gidan kuwa an saka masu kula da gidan ne, har dare babu al'amar sa, kwanciyar su suka yi abin su, hankali kwance. Ranar lahadi suka kuma tashi da aiki. Domin Nazifi ya tashe shi bayan ya tambaye su me suke bukata, kayan snacks suka rubuta mishi da su dangin zobo. Aikuwa ya amsa ya tafi can sai gashi kaya niki-niki. Sannan ta ce ya kunna musu injin. Cake da Donut suka yi, Rahilah ce keyi tana basu labarin yadda dangin Mahaifiyar ta, suke sonta. Sai dai har lokacin nan, babu me maganar sonta da aure saboda nakasarta. Gara Husnah an tsaya da maganar aurensu, dan uwansa Muhsin zata aura. Sai nan take tambayar su Kubrah, Husnah ta ce tun gama waec basu kuma haduwa ba. Haka suka cigaba da hira, bayan sun gama suka tafi wanka, dawowa tayi kitchen din daure da towel, domin ita ta bar musu dakinta ne, ta koma dakinsa tayi tayi wanka. Bata san da zuwansa ba, sai ji tayi yayi sama da ita. Ajiyar zuciya ta sauke tare da dafa hannun shi tana dariya. Bai tsaya da ita ko ina ba, sai dakinsa. Cikin wani irin kewarta yake tafiyar da ita. Kamar ya mai da ita cikinsa sai gashi daga ita har shi kuka suke, wani irin so yake mata, har ya samu nutsuwa, suka yi wanka a tare, yana goge wurin ciwonsa da ya dauko warkewa. Shafa wurin take tana kallon shi. "Kin ga aikin yayi kyau! Kin san waye ya bani huhunsa? Abdulhakim Sharif Hamidu." Tura kanta tayi gefen da babu ciwo tana murmushi. Haka suka shirya. A can main falo har da Abdul, wanda ya zauna kamar mara gaskiya, can sai Rahilah. Cike da mamaki suka yi ta kallon su, kafin suka shiga kitchen suna gulmar su. Basu ga Sa'ade ba, shi da kansa ya fito ya nufi dakin ta, ya dauke mata kaya masu kyau da babban mayafi, ya kawo mata ta shirya. Sannan suka fito a tare, kitchen ta shiga suka fara fito da abinci, Rahilah tana zolayarta. "Husnah ji yarinyar nan ashe shigewa suka yi wurin ita da mijinta" "da dai kun daina wannan maganar domin, Hammayo yana jin Yaren mu" zaro idanu suka yi. "Allah yasa ban ce kome ba" kallon Ra'is yayi cikin yarbanci ya ce. "Kasan yaran nan gulmar Lucky suke take gaya musu ina jin Yaren su." Kallon su yayi yana murmusawa, nan ya gayawa Abdul abin da yake faruwa da turanci. "Kai haba. " Nan suka gama shirya musu abinci, sannan suka bar wurin itama suka ci nasu a dakin su, sai murmushi take tana cin abincin. Kasa kasa Rahilah ya tab'a Husnah. Dariya suka mata, haka suka yi ta hira har suka gama da su Abdul zasu bar garin ne su fita da su Rahilah da Husnah, bayan Abuturab ya masu shatara na arzikn, nan gidan ya rage iya su biyu, da dare kuwa gidan su Inna suka nufa, basu dawo ba, sai dare. Suna dawowa suka wuce dakinsa. Anan suka yi wanka a tare. A wannan daren, sun gurji amarcinsu. Kamar me kafin suka kwanta. Sai da suka shafe sati daya, sannan suka wuce Umra daga sokoton, Ummi tasan dalilin sa na guje guje sarautar ce baya kauna, kuma dan kaniyar shi dole haka zasu koma yaje ya amsa. Daga Umra yawon buɗe ido suka yi ta yi, sai da Sultanah Badi'atul Noor ta mishi barazanar matukar bai dawo ba, wallahi sai ta kwace Sa'ade idan ya dawo. Haka ya hakura suka koma gidan, manyan fadar ne suka hadu, aka yi meeting. Sai bayan sun gama meeting din sannan suka nufi Badi'atul Noor da zancen. "Mun yanke shawarar akan Abdulrashid, zamu bashi sarautar dan masanin kwara, sannan an bashi auren Latifah yar gidan Khamal, mun samu Sahalewan haka ne daga Sultan Aliyu Abdulrahman Dan Aliyu sulu gambari. Ita kuma Saratu mun bada ita ga Ra'is Dawood, mahaifinsa ya maida shi mishi muƙaminsa na Waziri." "Masha Allah Ubangiji ya taya su riko. An yi haka da kwana biyu, Abuturab ya dawo. Yana dawowa Ummi ta amshi Sa'ade ta ce zaka yi ta ganawa da manyan mutane na tsawon kwanaki ita kuma zaka bar min ita. Murmusawa yayi ya ce. "Duk abinda kika ce Queen Mother " daga nan suka ajiye zancen ta mishi tass akan maganar bada auren yan matan da yayi ba da izinin iyayen su ba. "Haka kawai su nime yi min katsalandar cikin rayuwar aurena " "dama akan waec din Sa'ade na biya mata za a mata, kana ganin zata iya karatu da renon ciki?" "Kai Ummina me ya kawo zancen cikin nan?" "Ai na gani ne, shi yasa. Me yasa baka damu da zancen mutuwar mahaifinka ba?" Murmushi yayi me ciwo. "Ummina, naga mutuwan yayu na biyu akan Idanuna, sannan duk sun mutu ne domin Abba, idan nace ban damu ba nayi karya. Amma idan na barwa Allah zai gafarta musu, rike abin da aka maka bai janyo kome sai gaba da kullatar juna, shi yasa naki damuwa da mutuwar, Allah ya mishi rahama." "Amin Ya Allah, Ubangiji yasa mu dace." Bayan sati Uku aka yi bikin bashi sarauta, mutane dayawa sun zo har da su Inna. Dake basu san ana boye cikin Sa'aden ba ne Inna take tambayarta dama ciki da ita, shiru tayi, kafin kace me ai kuwa labarin ya karade ko ina, sai dai kuma a daren ranar zazzaɓi ya rufe ta, sai da aka saka mata ruwa. Tun daga ranar ta fara laulayi, don har su Inna suka bar garin bata cikin hayacinta. Haka har lokacin zana Jamb yayi, shima Alfarman aka nima mata, mijinta sarki kuma ya tafi da kansa ya zana mata, domin tausayin matarsa. Kaf dangi aka daurawa cikin nan kauna, Addu'a da rubutu babu wanda Ummi bata ba, har saukar Alqur'ani tasa aka mata akan cikin, da wahala ya ishe ta, sai ta Sa'ade na kuka wiwi,.ita a cire cikin wata biyar ta gaji wallahi. Dakyar Ummi suke lallabata. Kullum Zakiyyah da Rumaisah tare da Ummyn Aymana suna hanya, sai da ta cika wata bakwai cif ta daina laulayi, wanda yayi dai-dai da bikin Abdul da Rahilah, yaushe aka kulla, amma tabbas sun je har sokoto aka daura auren, aka dauko amarya daga yola, hannu bibbiyu Hajiya Ita amshi surukarta. A bakin Hajiya Daulah take jin labarin rabuwar Abdul da Sophia, tana can canada. An sha biki sosai. Kafin su bar garin Abuturab ya samu Dr Sharif inda ya nemi Alfarman ya dawo da Hajiya Daula, kuma be ki ba, haka ya dawo da ita.. --- Jingine da allon gado take, kafaffunta sun kumbura, kallon cikin wata takwas din da yayi turtsitsi yayi ya shafa cikin yana kallon yadda cikin ke motsi kamar zasu fito. "Sannu kinji" tun a scanner ake cewa biyu ne, kuma duk maza ne. Juyar da kai tayi tana jin azaba kawai. Gyara kafarta tayi zata sauka ya rike ta, "shaaaaaa!" Ruwa ya faso mata, komawa tayi ta zauna a jikin gadon. A rude ya riko hannunta. Zare hannunta tayi, tana nuna mishi waya ya kira Ummi. Ai bai kula waya ba, ya fita da sauri. A wannan yanayin ita kawai tasan ba su zasu cire mata ciwon ba, amma kuma kiran ummin zai taimaka mata. Yadda take zaune kamar ance ta ware kafarta, sai ga kan Yaro ya sako kai. Rike gadon tayi, Allah da ikonsa ya bata sa'ar Nishi sai ga ɗan kamar an zaro shi. Daidai shigowar su, "bani kayan haihuwar " Ummi ta fada, tana sauke Babyn tana mishi Addu'a. Sannan ta ajiye shi. Sake wani yunkurin tayi, sai ga Babyn nan ya kuma fitowa da mabiyansa, shima dauka tayi ta nema mishi tsarin shaidan. Sannan ta ajiye babyn, yanke cibiyar tayi ta nad'e su. Sake yunkurin tayi wani babyn ya fado yar karama da ita. "Allah sarki sun mata wayo" ta dauke babyn ta mata Addu'oin itama. Sannan ta jijjiga cikin sa'aden jini ya zuba, kafin ta kaita banɗaki ta zaunar da ita ta kuma zubar jini. Tana fitowa ta samu yana ta kiran su Ummyn. Tana zuwa domin tana Asibitin da take aiki da su alluran. Ummi ta gyara Uwar da yaran baki ɗaya, Ummyn Aymana da wata Dr suka zo, aka mata allura aka duba lafiyar yaran, Ummi ya kwashe su sai part dinta, can ɗakinta ta kaita, bayan ta sake mata wanka domin wanka sosai ta mata, Zuwairah ta kawo mata kunun kanwa da farfesun Bindin saniya. Tasha ta kwanta. Kafin wani lokaci labarin haihuwar ya karade ko ina, sai gashi, ana ta zuwa Barka. Inna daga Maikulki suka zo, ana jibi suna. Da yayun sa'ade, an yi hidima sosai irinta .manyan mutane, Yaran sun ci sunan Abubakar (Hassan sun bar mishi maina) Umar(Hussain sun bar mishi saraki) Dawlat khatoon (Gambo suna kiranta Amira) an sha hidima sosai. Domin jegon har da Sultan Abuturab ake yinsa domin cewa yake shima ya haihu ne, satin Inna Laminde biyu ta koma don duk sun tafi sun barta. A wannan aikin hajjin Bana Abdul iya biyawa Inna da Malam Aminu aikin hajji, domin yayi alƙawari ne ya sauke. Watan su Sa'ade uku ta koma bangarenta bayan Ummi ta gyara ta ciki da waje. Zo kusa rawan kai da rawan jiki. Sai da suka cika wata hudu har sun fara zama suka tafi Sokoto wanda yazo daidai da bikin Husnah. Anyi bikin da sati daya Rahilah ta haihu, Abin mamaki sunan Sultanah Badi'atul Noor aka saka. Takanas tazo sunan da kayan takwaran ta. Sai bikin Yusuf da aka yi a lokacin Allah ya bawa Aunty Ummi ciki. ----- A can kwara ma buki aka yi sosai, sannan aka bawa Kowa sarautar da ta dace da shi, Ra'is da Abdulrashid. Sultanate tana kwance babu abinda ba a mata, sai dai tana wulakance domin tana gani babu yadda ta ita, sai takaici da bakin ciki. Badi'atul Noor ita ta amshi kome abin da yake tsoro, gashi ya faru sauran matan Sultan Abdulrahman, tunda aka raba gado kowa ta kama gabanta. Yaran su Abuturab ya dauke nauyin su har da na Yayunsa. **** Bayan shekara biyar, bikin Yaye daliban babban Jami'ar Jos take, a cikin har da Fulani Sa'adatu Aminu,matar Sultan Aliyu, cikin ikon Allah ta fito da First class, a bangaren Jarida, sai tafa mata ake, idan ja ganta sai ta burge ka, yarinya me ji da kuruciya ga Yaranta nan biyar ta kuma haihuwar wasu Yara biyu. Bayan an gama raba musu kyautattaka. Suka bar makarantar. Har zuwa lokacin Allah ya bai bude mata baki ba, Ƴaranta da ta haifa na baya mace da namiji. Macen sunan Innarta ce ana kiranta da Qurratul Ayn, namijin Amir ake kiransa. Tunda suka shiga private jet, Abuturab sai Binta da idanun yake. Karshe da ta zauna kusa da shi ya ce mata.."Kin san Allah, london zamu wuce na dasa miki Ummina, domin naga sai wani Yanga kike min" juya kanta tayi tana dariya. *** Malam Aminu duniya sabuwa, sai gashi har da karo aure, inda ya hadu da wata munafukan bazawara, ta hada shi da cutar sanyi. Dama can Inna ta yafe shi. Ai haka ya hana kowa sakat, abin haushin da dariya ya gogawa Inna Larai, haka suke ta jinya a tare. "Allah ya tsinewa, Jummala, munafuka na gode da ba sida ta saka.min ba" "Babu tsinuwar da zai ka mata, kwadayi da jarabarka" ** Husnah ta haihu da namiji, haka ma Aunty Ummy ta haihu itama da namiji, Matar Yusuf kuma Y'a mace, lokacin Sa'ade suna London ganin likitan kunne ko za a dace. Amma har zuwa lokacin ba A dace ba. ALHAMDULILLAHI. (Kun gane ba kome kake so zaka samu ba, Matsalar sa'ade na bar shi a haka ne, tana ji tana gani magana ce Allah bai nufa tayi ba, idan muka ce lallai sai tayi magana tow kuwa mun ja da ikon Allah, Don Allah ayi hakuri Haka na tsara labarin ba zata tab'a magana ba, sai dai kuma she achieve more successful abubuwa, ta samu miji me sonta, Dangin mijin nasonta Mahaifiyar miji na sonta. Alhamdulillahi, Don haka idan kuna da interesting kuyi following din Karfe dukka karfe ne, Na gode taku har kullum Ramlat Abdulrahman Manga Mai_Dambun gayu.)