[11/25, 3:54 PM] Rano2: Sanadin               Labarina                    Free Page (1) ©®Hafsat Rano ****Gudu take a cikin ruwan da ake tsugawa kamar da bakin kwarya, kokari take ta kai gidan kafin duhun magriba ya sakko, duk da shekarun ta ba zasu wuce sha hudu zuwa sha biyar ba, amma haka ake aikenta har gaba da  in da taje a yanzu,ba yau ne karo na farko da ruwa ya fara tare ta ya zane ba, ba kuma shine zai zama na karshe ba, duk da haka har yau ta kasa sabawa da dukan ruwan, duk sanda ya tabata toh fa sai ta kwanta rashin lafiya amma hakan ba zai hana idan wani hadarin ya sake hadowa a sake aiken nata ba. Daidai wajen wani shago tazo wasu manyan mutane da suka fake a wajen suka ce tazo ta fake, kallon su tayi kawai ta cigaba da gudu a cikin ruwan dan idan har ta yarda ta fake din toh bayan dukan ruwan za'a kara mata ne da dukan gaske, shiyasa ta gwammace ruwan ya dake ta akan dukan Iya Lami wanda a duk sanda ta dake ta sai ta sha matukar wahala, bayanta duk shatin dukan ta ne da kafafun ta, shiyasa take matukar tsoron abinda zai hado su da ita.    Tana cikin gudun takalmin ta ya tsinke, ta durkusa ta cire su dukka ta rike a hannu ta cigaba da falfala gudu. A zauren gidan nasu ta tarar da iya Lami tana hura wuta, wani kallo tayi mata wanda ya saka hantar cikin ta kadawa, tayi saurin cewa "Wallahi ita ta tsaida ni, sai da aka samo chanji kafin nan kuma har an fara ruwa." Ta fada tana rawar sanyi hakoranta na hadewa waje guda. "Bani." Tace tana mikowa hannu, hannun na rawa ta mika mata ta warta tana hararar ta "Shegiya me zubin mayu, wuce kije ki cire kayan nan kizo nan,kin tsare ni da shegun idanuwan ki kamar na kura." Da sauri ta shige ciki tabi gefe ta shiga dakin ta, ta cire kayan ta shanya su akan kofar langa-langar dake dakin sannan ta saka wasu, har cikin kashin ta take jin wani irin masifaffen sanyi, amma haka ta sake fitowa ta koma zauren, ta samu gefe ta durkusa ta hau tankad'e, tana yi tana gyara wuta, ta gama ta rud'a sannan ta koma gefe ta hade kanta da guiwarta zazzabi na neman rufeta.    Ji tayi an duma mata dundu, ta dago da sauri tana kallon Iya Lami akanta "Dan ubanki shine zaki yi min talgi ruwa ruwa, ki hade kai da guiwa kina ji har ya soma zubewa dan rashin mutunci kiyi kamar baki sani ba?." Da sauri ta kalli wajen tukunyar, ta mike da sauri ta hau gyarawa tana rage wutar baya, kwafa tayi ta sake ficewa lokacin ruwan ya tsagaita sai dan yayyafi da ake yi, a gaban wutar ta zauna dirshan har ta gama tuwon ta kwashe, ta maida ruwa akan tukunyar da zata gasawa baffanta kafarsa.    Tana zaune ruwan yayi ta kwashe kwanukan tuwon ta shigar dasu dakin iya Lamin sannan ta samo baho ta juye ruwan ta dauka ta shiga dakin Baffan da sallamar ta, yana kwance akan yar katifar sa, ransa babu dadi tunda aka fara ruwan yake ta tunanin ta, ganin ta yanzu ya sakashi sauke ajiyar zuciya "Bongel..." "Na'am Baffa " "Kin dawo ashe, ruwa ya taba ki ko?" Girgiza kai tayi "A ah yayyafi ne kawai." "Alhamdulillah, ina ta tunanin ki tunda naga an soma ruwan nan, kiyi hakuri kinji?" Shiru tayi kawai, ta jawo tsumman da take gasa masa kafar ta soma danna masa kamar yadda iliya ya koya mata. Ta gama ta fitar da ruwan sannan ta dawo ta zauna a gefen sa, cikin tsananin tausayinsa, tun bayan da akayi masa aiki a kafar ya zamana duk damuna kafar na tashi har ta hanashi takawa kwata-kwata, ita take kula da fiye da rabin dawainiyar sa Iya Lami babu abinda take sai yi masa fada da masifa kullum ita ta gaji da dawainiya dashi da yar sa, baya tanka mata dan yana tsoron tace zata tafi, abubuwan zasuyi musu yawa shi da yar sa, shiyasa yake lallabawa baya taba mata musu ko yayi jayayya da ita.    Shigowa tayi dakin dauke da kwanukan tuwo da miya, da sauri ta tashi ta karbe ta, ta ajiye a gefen baffan sannan ta raba ta fice daga dakin, ta nufi dakin ta, ta kwanta akan tsohuwar katifar ta, ta lulluba da wani zanin mahaifiyarta, duk da haka bata daina jin sanyin ba, amma babu yadda ta iya, haka ta cigaba da rawar sanyin har dare ya soma yi sosai, kafin ta samu bacci me nauyi ya dauke ta.      Da safe ta tashi da ciwon kai, duk da haka sai da tayi duk ayyuka kanta, ta koma dakin bayan ta gama ta kwanta kenan Iya Lami ta leko tace ta tashi, tazo ta debo ruwa, ba musu ta saka wani tsohon Hijab dinta, ta fito ta dauki bokitin ta fita. Dakin da baffan yake ciki Iya Lami ta leka, ya kalle ta yace "Lami nace a daina saka yarinyar nan dibar ruwa dan Allah." "Idan bata debo ruwa ba kai ne zaka debo? Eh?" Shiru yayi ganin ta harzuko masa "Da me zan ji? Da wahalar ka ko tata? Ko ni kake so na debo ruwan da kaina ne!?" Ta cigaba da fadan tana fita tsakar gidan Be amsa mata ba, ta dinga sababi har sai da yaji dana sanin yin magana, haka yana ji yana gani sai da ta cika gidan tas sannan Lamin ta kyale ta, ta sake komawa dakin ta kuma kwanciya kanta na sake matsa mata sosai, ga wata mura da tazo ta chunkushe mata hanci da makoshin ta. Har wajen azahar Jiddan na kwance bata fito ba, tasan dukan ruwan ne ya sakata zazzabi amma tayi biris kamar bata sani ba,ta cigaba da sabgar ta bata damu da halin da zata shiga ba, ko dubo ta batayi ba har sai da Saude ta shigo dauke da kanin ta Muhusin a kafardar ta, ta gaida Iya Lamin sannan tace "Inna ce dama tace muzo muji ko lafiya Jidda bata leko yau ba?" "Jeki dakin ta ki dubo." Tace tana yin gaba ta cigaba da sabgarta, dakin ta shiga ta sameta a kanannade ta chure waje daya, ta lulluba da tsuman zanin ta. "Jidda, jidda?" Tace tana janye rufar. "Sanyi nake ji Saude, rufe ni." Maida mata rufar tayi, ta zaunar da Muhsin a gefenta sannan ta fita, taje ta sanarwa da Babar tasu sai gasu sun dawo tare, a zaure Iya Lami ta tsaida su. "Lafiya Asabe?" "Lafiya lou, Jidda nazo dubawa Saude tace min tana kwance bata da lafiya." "Me zaki mata toh? Ko tsabar kinibibin da kika saba ne, salon a cigaba da zagi na a gari ace bana kula da ita." "Kina kula da ita din ne? Kiji tsoron Allah wallahi Lami, Allah kuma sai ya tambaye ki wallahi, "Abinda naga dama shi zanyi a cikin gidan nan, kamar yadda babu shegn da ya saka miki ido akan gidanki haka nima babu shegen da zai zo min da iyayin banza da wofi." "Kinsan mutumin da be haihu ba, ba lallai yasan daraja da zafin d'a ba,kuma dole naje naga halin da yarinyar mutane take ciki dan ke bakar azzaluma ce baki san rayuwa ba." Magaanar tayi mugun yi mata zafi, tayi kokarin warto rigarta da nufin su daku amma ta goce tayi shigewarta dakin da Jiddan ke ciki, ta taimaka mata ta mike tsaye, ta riketa suka fito, bayan su ta biyo tana huci kamar zakanya tana zage-zage amma tayi mata banza sai da suke fice daga gidan. Gidan ta, ta kaita ta dora ruwa ta sakata tayi wanka, ta bata kayan Saude ta saka sannan ta bata abinci da paracetamol ta sha, ta kwanta lamo abin tausayi, duk wanda ya rasa uwa yayi kuka dan tabbas yayi babban rashi a rayuwa. Yamma likis zazzabin ya sake rufe ta, ta saka aka samo machine a chan hayi yazo ya dauke su tare, ya kai su chemist din cikin garin,akayi mata allura aka bata magunguna sannan suka dawo, ko da suka dawo bata barta ta koma ba,tace tayi kwanciyar ta anan har sai ta samu sauki, ta aika Saude ta fada wa baffan zata kwana a gidan su, yayi godiya dan hakan yafi masa sauki kuma hankalin sa yafi kwanciya. Cikin dare ya kasa rintsawa, tunanin irin rayuwar da yar sa take ciki ya dame shi, be san ya zai yi ya samar mata ingantacciyar rayuwa ba a halin da yake ciki, irin rayuwar da mahaifiyarta tayi mata shaawa, duk da haka ba zai zauna ya zuba ido Lami ta lalata masa rayuwar ta ba. Ya dade yana sakawa da warwarewa ya rasa mafita haka ya hakura ya kwanta har bacci yazo yayi awon gaba dashi. Da safe ta tashi da dan kwarin jikin ta, har ta taya Saude yan aikace-aikacen gidan duk da ba masu yawa bane, bayan sun karya suna zaune yar karamar wayar Innan tayi kara alamun shigowar kira, da sauri ta shigo dakin tana fatan ya kasance wadda take jiran kiran ta ne. Ita din ce kuwa, jiya tayi mata flashing bata biyo ba, sai yanzu da safe dama tayi tunanin bata gani ba, waje ta fita zuwa dakin baffan su Saude ta turo kofar saboda bata so suje magaanar da zasuyi. Sallama sukayi wa juna sannan suka gaisa da tambayar bayan rabuwa, sai kuma ta dora da "Dama kiran da nayi miki akaan magaanar Hauwa'u ne, ina ganin lokaci yayi da zaki tuntubi B weaffanta da magaanar nan da mukayi kwanaki, a wannan gabar ba lallai ya hanaki ba, dan magaanar da nake miki ma yanzu haka a gidan nan ta kwana, bata da lafiya amma ko a jikin tsinanniyar matar chan, gwara kawai kizo yayi hakuri ki tafi da ita." Shiru tayi, alamun maganpma take itama daga dayan bangaren, tana dai ta amsawa da eh, sai kuma tace "Hakuri zai, idan da rai da lafiya watarana da kanta zata zo har in da yake." "Yawwa kin gani, kizo dan Allah ko zuwa gobe ne, zan barta anan din har zuwa goben idan kin tabbatar da zuwan naki sai ki sanar min, akwai abubuwan da zan bata ta tafi dasu." "Toh shikenan a gaida yaran da Maigidan." Soke wayar tayi a zanin ta bayan sun gama, ta fito zuciyar ta fes, tana kuma fatan idan Innajon tazo ta samu tafiya da ita chan in da take aure, a kalla zata huta da wahala rayuwar ta zata sauya, ko da sanadin labarinta ne, idan mutane suka ji zasu tausaya mata. ***Wunin da tayi a gidan su Sauda ya sa ta kusan mance rayuwar da take a cikin gidan mahaifin ta, har tana dariya da hira tamkar ba ita ba, gabannin magriba aka sake kiran Innan ta amsa cike da jin dadi, bayan sun gama wayar ta dinga murna tana fatan hakan su ya cimma ruwa, da daddare bayan sun gama cin tuwo ta dauko wata yar karamar jaka, me dauke da sarkar kafa da ta wuya, jikin su dauke da tambarin zuciya da wani abu kamar ganyen bishiya, mika mata tayi tace "Wannan shine abinda mahaifiyar ki ya bar miki Jiddah, ki adana su watarana zasu miki amfani." Karba tayi tana dubawa kafin tayi murmushi kawai, bata ce komai ba ta damke su a hannun ta, tana jin wani irin yanayi mara misaltuwa. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107 [11/25, 3:54 PM] Rano2: Sanadin                Labarina               Free Page (2) ©®Hafsat Rano ***Rayuwar ta tun bayan da ta bude ido ta ganta a gaban baffan ta, bata san wani abu daya danganci mahaifiyarta ba, bata san wacce irin rayuwa mahaifiyar ta tayi ba har zuwa ranar da ta koma ga mahaliccin ta, ranar da ta zama silar zuwan ta duniya itace ranar da tayi silar mutuwar ta. A duk lokacin da ta bukaci sanin wani abu na daga sashe na rayuwar ta sai Baffa yace mata ba yanzu ba, sai ta girma ta mallaki hankalin kanta. Ta kan yawan tuna mahaifiyar ta duk da iyakar sanin hoto kawai tayi mata,amma ta gaza manta zanen fuskarta a cikin zuciya da kwakwalwarta. A yau da ta samu wani abu da ya danganci mahaifiyarta sai taji tamkar ta san wani sashe na labarin ta, wani sashe me matukar muhimmanci a kundin rayuwar ta. Sake damke su tayi da kyau, ta samu kasan kayan ta, tayi musu boyo me kyau, irin boyon da zaka yiwa duk wani abu me matukar muhimmanci a gareka. Gidan su ta shiga kanta tsaye cike da karsashin ganin ta, tayi saurin fadawa kanta cike da murna da dokin ganin ta, rungumeta tayi a jikin ta tsam zuwa wani lokaci kafin ta saketa tana dariya "Jidda." "Na'am..." Ta amsa cike da zumudi sannan ta zauna a gefen ta, "Ya jikin naki?" "Da sauki." "Sannu. Allah ya kara sauki." "Amin." Ta amsa sai ta mike, taje ta kawo mata ruwa sannan ta fita zuwa dakin ta, ta tura kofar ta shiga ta soma harhada kayanta waje daya, zuciyar ta cika fal da farin ciki. Kasancewar kayan ba masu yawa bane yasa ta gama hade su kaf, ta fito zata koma taji suna magana da Baffa sai ta fasa ta samu waje ta zauna har sai chan da aka kwala mata Kira, ta tashi da sauri taje, Baffa yace ta dauko kayanta tazo. Zama tayi a gaban baffan ta tankwashe yar kafarta, kayan ta dake cikin yar karamar ghana most go ta sake rik'ewa gam tana sauraron maganganun dake gudanuwa tsakanin Baffan da Innajo. "Jidda amana ce a wajenki Innajo babu yadda zan yi ne amma da babu yadda za'a yi na rabu da ita, sai dai tana bukatar kulawar uwa a halin yanzu, dan haka na baki amanarta, idan kika ci amanarta ba zan yafe miki ba, ita din marainiya ce, bata san mahaifiyar ta ballantana wani dangi na kusa, ni kadai ne gatanta, sai ke yanzu da na damka miki amanarta a hannunki." "In sha Allahu zan rike amana, nagode nagode da karamcin ka gareni, in sha Allah Jiddah ba zatayi kuka ba, kuma nayi alkawari duk sanda akayi hutu zan kawo maka ita nan, nayi wannan alkawarin." "Shikenan,ubangiji Allah ya baki ikon rike amanar da kika dauka." "Ayi dai mu gani idan iska zata hura wuta." Lami tace tana daga kan kofar dakin ta, kallon ta Baffa yayi ya girgiza kai kawai, itace ummul'aba isin da yasa zai bawa kanwar tasa Jidda, ba dan haka ba babu yadda zai ya rabu da ita dan ganin ta kadai yake rage masa kewar marigayiya, amma babu yadda ya iya, hakan shine maslaha akan irin kuntacacciyar rayuwar da Jiddan take fuskanta a cikin gidan mahaifin nata a gaban idon sa bashi da ikon hanawa ko tsawatarwa saboda lalurar da ta sameshi ta ciwon kafa. "Ku tashi ku tafi kar kuyi dare a hanya, Allah ubangiji ya kaiku lafiya." "Amin Baffa." Tace cikin yar siririyar muryarta da take nuna tsantsar yarintar ta "Allah ya kiyaye kinji? Ki rike abinda na fada miki kar kiyi wasa dashi, in sha Allah ba zaki yi kuka ba." Da kai ta amsa masa, ta mike Innajon ta mika mata hannu ta karbi kayan, sannan tace "Zamu tafi Lami, sai ki zuba ruwa a kasa kisha, kuma in sha Allah sai mugun nufin ki ya koma kanki." Abun ka da me jiran kiris sai gata a tsakiyar tsakar gidan tana huci tayi kan ta "Ke har kin isa ki fadan magana? Waye be san rayuwar wahalar da kike a gidan miji ba, bora wadda bata da maraba da yar aikin gidan." Wani kallo Innajo tayi mata, maganar tayi mata mugun ciwo amma sam sai taki nunawa, ta rike hannun Jiddah ta soma tafiya "Yaya mun tafi, Allah ya kara lafiya." "Amin, Allah ya tsare, ki kirani da zarar kun sauka dan Allah." "In sha Allah." Cikin daga kafa suke fice daga gidan, ya saka hannu ya share guntun hawayen da suka zubo masa, kansa a kasa yana sauraren maganganun da Lamin take ta farfad'a cikin daga murya dan Innajon ta jiyo ta. Sai da taji tashin motar su sannan ta shiga daki tana cigaba da sababi. ***Mota ce irin golf din nan Alhaji yayi mata shatar ta, su biyu ne a bayan motar lokaci zuwa lokaci sai ta kalli fuskar Jiddah tayi mata murmushi, maganganun Lami sun yi matukar tasiri a zuciyar ta, bata da maraba da bora kamar yadda ta fada amma ya zatayi? Ta ta kaddarar kenan, zata jira zuwa lokacin da Allah zai kawo mata dauki ko ta samu sauki a zuciyar ta. Tafiya ce ta kimanin awa daya da rabi sannan suka iso, daf da magriba me motar ya sauke su a kofar gidan, idanun Jidda suka fito waje tana kallon in da suka zo din, gida ne matsakaici me bakin gate, tura yar karamar kofar dake jikin gate din tayi hannun ta daya na rike da kayan Jiddan daya kuma hannun Jidda ne. Abu ce ta fara ganin su, ta taho da sauri ta karbi kayan hannun ta sannan tace "Sannu da hanya Anty " "Yawwa sannu Abu." Ta amsa sannan ta cigaba da tafiya zuwa wata kofa dake kallon gabas, irin kofar nan me hannu biyu,da glass me kauri a tsakankanin kowanne waje, duhun magriba ya mamaye babban falon nasu Amma duk da haka kana iya ganin mutane a zazzaune, sallama tayi yaran suka amsa, dama kuma su din ne zasu amsa uwar gayyaar ko kallo bata ishe ta ba, tana hakimce a saman kujera cikin yanayin rashin jin dadin ganin su. "Anty sannu da zuwa." Yaran suka shiga jera mata sannu, Usman da Muhammad suka taso da gudun su, suka rungume ta, ta daga su sama daya bayan daya tana dariya. "Anty wace wannan?" Amira ta tambaya tana leken fuskar Jidda da ta rakube a bayan Antyn. "Ina ruwan ki Amira? Bana son shishigi fa." Hajjajun dake hakimce ta tsawatar mata tana jan tsaki, murmushi Antyn tayi kawai ta girgiza kai sannan tace "Yar uwa kuma kawa na kawo muku Amira, gata nan sunan ta Jidda." Shiru Amiran bata ce komai ba tana tsoron sake magana tasan halin Mama sarai zata iya bugunta akn haka. "Muje Jidda, naji ma an soma kiran magriba." . Suka wuce su zuwa wani dogon corridor da zai sada su da bangaren Antyn, daidai lokacin aka kawo wuta, Abu ta ajiye kayan Saudan sannan tace "An gama tuwon Anty, na fadawa Mama dai a zato na ko har na tafi baki dawo ba." "Sannu da aiki, kin yi saurin gamawa ma." "Wallahi, gani nayi garin damina, gwara kayi da wuri kafin ruwa ya sakko." "Gaskia kam." "Akwai abinda zaa yi ne kuma?" "Umm, babu gaskia,zaki tafi ko?" "Eh idan ba abinda za'a yi ba." "Babu, bari na diba miki yar tsarabar kauye ba dai yawa." "Aikuwa nagode Anty." "Zo Jiddah." .. Ta yafito ta da hannu, suka shiga daya daga cikin dakuna ukun dake dan madaidacin falon Antyn. "Ga dakinki kinji, zauna bari na sallami Abu nazo sai na nuna miki yadda komai yake, ki saki jikinki kinji?" Da kai ta amsa tana kallon dakin, fita tayi taje ta sallami Abun sannan ta dawo tace tayi alwala, itama taje dakin ta, tayi alwala sukayi sallar a tare, sannan ta kunna mata kallo tace tana zuwa. Part din Maigidan ta nufa bayan ta dora ruwa a saman gas din dake kitchen din bangaren nata, ta gyara masa dakin duk da kafin ta tafi ma sai da ta gyara amma tasan da gayya Maman zata bata musamman toilet, haka ko yaushe take sake gyarawa idan zata shiga ta bata sau dubu bata kuma taba tanka mata ba, yau din ma sai da ta sake gyarawa ta kunna turare sannan ta fito, ta dawo ta samu ruwan ya tafasa ta cika flask sannan tayi masa tuwon alkama wanda zai ci yanzu da kuma safe, ta zubawa Saudah a ciki ta kirawo ta kitchen din duk dan ta sake da ita, ta karba ta fita, Usman da ya gama zaman falon ya shigo ya haye kafar Jidda yana mata magana "Kece Yayarmu da Anty tace zata kawo mana ke?" Gid'a masa kai Jidda tayi, sannan tayi masa murmushi "Zaka ci tuwo?" Tace masa tana kallon plate din dake gabanta. "Naci tare da Muhammad, amma zan kara naki." "Toh muci." Ta tankwashe kafarta shima sai yayi yadda tayi, suka shiga cin tuwon a tare, har suka gama Anty na ta kaiwa da komowa a tsakankanin bangaren Maigidan da nata, sai da ta gama hada masa komai sannan ta nutsu ta zauna taci abincin ta watsa ruwa dan a gajiye take jin ta sosai dan ba wani zama tayi ba tunda suka shigo. Wajen takwas da arba'in Baban ya dawo, sun idar da Isha Usman yayi bacci, Antyn tace itama Jiddan taje ta kwanta, ta rakata har daki ta nuna mata duk abinda zata bukata ta kawo mata ruwa saboda dare sannan ta dauko Usman ta dawo dashi dakin tayi musu addua sannan ta kashe musu wutar dakin ta nufi bangaren Baba. ***A zaune ta samesu da Mama, ta bararraje tamkar kwananta ne ranar, ta bude masa abincin har ya soma ci yana bata labarin kasuwa, wani banzan kallo maman ta watsa mata, tayi tsaye ranta na sosuwa da abinda ake mata, dagowa yayi ya kalle ta, "Halima, karaso mana kika ja tunga anan, kinga yayarki ko? Wai kin sha wahalar hanya shine take taimaka miki da wannan babban aikin." Yake tayi ta karaso ta zauna daga kubin damar sa, ta gaishe shi a ladafce ya amsa mata yana tambayar yadda ta baro su "Ina fatan dai kafar Yaya da sauki." "Alhamdulillah dai toh. "Allah ya bashi lafiya, zan yi kokari a weekend din nan naje na sake dubo sa, ina yar taki? Kin taho da ita ice ko?" "Eh tayi bacci." "Ok madallah, na ganta gobe idan Allah ya kaimu." "Amin." Tace sai ta mike ta shige bedroom din ta zauna a sanyaye, sama-sama take jiyo hirar su har wajejen goma na dare sannan taji tafiyar Maman. Kwanciya kawai tayi dan babu kuma bukatar ta sake komawa falon. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107 [11/25, 3:54 PM] Rano2: Sanadin              Labarina                                    Free Page ( 3) ©®Hafsat Rano *** ***Kiran farko akan kunnen ta, saboda yadda jikinta ya saba da tashin wuri, dan tun bata iya tashi ba har ya zame mata jiki, ko bata ji kira ba zata mike, wataran ko sallah Lami bata barin ta tayi zata fara sakata aiki, itace dauko itace, itace debo ruwa da sharar gidan baki daya dan duk sai tayi su kafin ta tafi makaranta wadda take da yar tafiya tsakanin su, haka ta saba ta goge tun shekarun ta basu kai haka ba, babu wani aiki da yake bata wahala sai dai idan ba sunan sa aiki ba. Zama tayi jugum tana kallon yanayin dakin, ta kalli Usman da yake bacci a gefenta, tana matukar son yara, haka take ko a gida bata da aiki sai jajibo yaran makota kafin Lami ta hanata. Turo kofar akayi, Anty ta shigo sanye da Hijabi, ganin ta a zaune ya bata maki "Har kin tashi Jiddah?" Tace tana karasowa cikin dakin "Tun dazu na tashi." "Toh maza tashi kije kiyi alwala muyi sallah, Usman be yi kuka ba ko?" "A ah be yi ba." "Toh yi alwalar maza kizo muyi sallah." "Toh." Tace ta sakko, taje tayo alwala suka fara yin raka'atanil fajr sannan sukayi subh. Al'kurani ta dauko suka fara daga Falak da Nasi, zuwa in da Jiddan ta tsaya a karatun, ta yaba sosai da yadda take karatun dan batayi tunanin hakan ba duk da baffa ba daga nan ba wajen riko da addini. Suna zaune tare har garin yayi sha, tace mata ta koma ta kwanta, ita kuma ta fita zuwa shashen Baban dan tasan zuwa lokacin ya dawo daga masallaci. Tana fita ta fito itama ta je kitchen ta dauko tsintsiya da faka dan ko ta kwanta ba wai iya baccin zatayi ba, bata saba ba, ta share falon tas ta gyara kitchen ta wanke kwanukan da suka bata jiya da daddare sannan ta wanke toilet, bayan ta gama usman ya tashi, ta rakashi bandakin tayi masa alwala da brush sannan tace yayi sallah, be iya ba tunda karami ne haka yayi tana kallon sa.   Wajen takwas Antyn ta dawo shashen sai dai tsananin mamaki ya kamata, ganin yadda ta gyara ko ina kamar ba ita ba, murmushi kawai ta dinga yi tana wa Allah godiya da ya duba ta ya bata 'ya me taimaka mata. Kunun da Abu ta dama tazo kawo wa kawai taga yadda ta gyara ko ina, albarka ta dinga saka mata sannan tace taje tayi wanka zata je ta gaida Baba idan sun gama karyawa.    A babban falon suke karyawa gaba dayan su, har Baban dan yace cin abinci a tare yana kara shakuwa, shiyasa suke zama kowa yaci da dan uwansa musamman weekend da baya fita da wuri sai rana ta daga. Fitowar ta kenan daga wanka ta gama saka kayanta tana goge ruwan da yake akan fuskar ta Amira da ta sato hanya ta leko dakin fuskarta a sake, "Kawata." Tace tana sako jikinta cikin dakin "Amira." Ta kira sunan ta da taji Antyn ta fada jiya, hakan yayi ma Amiran dadi "Jiddah ko?" Kai ta daga Mata "Kizo muje mu karya, kinsan gaba daya muke yin breakfast har Baba." "Hadda ni?" "Eh, kema kin zama yar gidan nan ai, taho muje." Ta ja hannun ta suka fito, bata so ba dan tana da jin kunya sosai da rashin saurin sabo, bata kuma saba da mutane da yawa ba daga ita sai baffanta sai Inna Lami. Sun firfito dukkan su kowa na zaune wasu a kasa wasu a saman kujera, su biyu ne mata a zaune Maryam, sai Safiyya wajen su Amiran ta jasu, tace "Ya Sofy, Mero, ga Jiddah." "Sannun ta." Safiyyan tace tana danna wayarta, babba ce dan da alama duk ta girme su,  murmushi sauran sukayi mata hakan ya sakata sakin jikinta kadan ta zauna a gefen Amiran ta makale. Maman su ce ta fito ta wata kofa taci ado sosai, kamar wadda zata tafi gasar kyau, babba ce dan akalla shekarun ta zasu kai arba'in da biyar amma ba zaka taba cewa ta kai ba saboda gyara da kyawun jiki. Duk suka gaishe ta ta amsa idon ta akan Jiddan, da sauri tace "Ina kwana?" "Lafiya lou bararoji." Tace tana wucewa kujerar da Muhammad da Usman suke zaune, Suka tashi ta zauna tana hararar Amira. Bararojin ne ya dinga yawo a kwakwalwarta har akayi sallama aka shigo falon. Baba ne ya shigo Anty na biye dashi itama tayi wanka sai dai shigarta very simple ba kamar Mama ba, gaishe da Maman tayi da yake a gaban Baba ne ta amsa a sake, zama sukayi dukka sauran yaran suka gaida Antyn da Baban itama sai tabi sahun su ta gaida Baban. "Zo 'yata,yanzu nake shirin tambayar ki dama." Tashi tayi a kunyace taje gabansa ta durkusa ya shafa kanta "Ki saki jikinki kinji, nan gidanku ne ga yan uwanki nan dukkansu,duk abinda kike bukata ki sanar dani kinji?" Daga kanta tayi alamar toh, ya sake shafa kanta yace "Yawwa, Allah yayi muku albarka baki dayan ku." "Amin." Suka amsa gaba daya, ran Mama ya baci sosai amma bata so ta nuna ta danne tana kallon Safiyya da itama ita take kallo. "Maryama jeki kira yayanku, bansan me suke ba na kuma fada musu da wuri zamu fita." "Wani wajen zaku ne?" "Eh zamu je a dauko Yaya, hutun ya isa haka gashi lokacin komawa ganin likitan ta yayi." "Gaskia." Tace a kasan ranta kamar ta kurma ihu, bata san zaman Yayan tare dasu musamman tun bayan da ta tirsasawa Baban ya kara aure tun daga sannan ta tsane ta, dan tun asali dama Yaya bata son ta, shiyasa sai da tayi yadda tayi ta saka ya auro mata wadda ko a mafarki bata taba kawo ta a matsayin kishiyar ta ba,yar kauye kuma yar talakawa, ita din yar masu kudi ce sannan tana business dinta tana samun kudi sosai, tun daga sannan ta kullaci Yayan, tafiyar da tayi tsawon wata guda ya bata damar sakewa a cikin gidan, jin zata dawo yanzu ya saka ta kasa ko sakewa taci abincin, ta tashi tace zata tafi, Safiyya ce ta rike mata jaka suka fice tare. A harabar gidan ta hadu dasu, Fauwaz ne a gaba sai shi a baya yana nannade hannun rigar sa zuwa sama, kansa kasa fuskar sa babu yabo babu fallasa Safiyya ta kira sunan sa ganin zai wuce su "Ya Tariq!" Tsayawa yayi yana kallon ta, kafin yace "Mah, fita zakuyi?" "Eh, zamu je cikin gida." "This early?" "Past 9 fa, kai kake ganin yayi wuri." "Ok a gaida su." Ya sa kai ya cigaba da tafiya zuwa main part din, mota suka shiga Fauwaz ya bi bayan sa, ya sameshi har ya zauna a gefen Baban suna magana, Zama yayi shima ya gaishe da Baban dan shi kadai ya rage a falon duk sun shige ciki. Breakfast din sukayi a tare, sannan Baba yace Tariq yaje ya sauya zuwa manyan kaya, ba a san ransa ba ya chanja zuwa shadda dinkin rigar da kadan ta wuce guiwar sa, ya rike hular a hannu ya fito yana jin shi a takure.    Cikin gidan ya shiga, ya bi corridor din da zai kaishi part din Antyn, ya shiga bakin sa dauke da sallama kasa-kasa. Su uku ne a zaune a falon, Saudah, Amira da Umaima. Fitar Mama ya basu damar biyo Saudan suka zauna suna janta da hira, Amira ta saka musu waka suna ji ya shigo, a rikice ta danne power botton din wayar ta kashe ta gaba daya, kallon ta yayi ,yayi kamar be ji komai ba, ya wuce ya zauna a cikin daya daga kujerun falon yana ciro wayar sa. A tare suka hada baki da Umaima suka gaishe shi, yayi kamar be ji ba, yana cigaba da danna wayar sa. Sum sum sum suka fice ya zama sai Jiddah kawai a falon "Ke je ki kira min Anty." Yace be ko dago ba, ta mike ta nufi dakin Antyn ta kwankwasa, daga ciki tace mata ehem alamun tana toilet, dawowa tayi ta tsaya daga bayan kujerar tace "Tana bayan gida." Dagowa yayi jin abinda ta fada, sai a lokacin ya ganta, fuskarta fiki fiki, yar firit kamar ka hureta ta fadi saboda rama, mamaki ya kamashi ganin ta "Wacece ke?" Yace yana kafe ta da ido, sosai ta duburburce ganin yadda ya kafe ta da ido, idanun sa manya sosai masu ban tsoro "Na'am?" Tace cikin hada kalmonin "Who are you? Daga ina kika zo?" Ya sake tambayar ta har lokacin kallon ta yake,be taba ganin ramammiya karmashashiyar yarinya irin ta ba, shi ya zata ma aljana ce, saboda tsabar rama har wani rami ne a fuskarta ya shiga ciki. Bata san amsar da zata bashi ba, sai kawai tayi shiru tana wasa da hannun ta. Anty ce ta fito a daidai lokacin "A ah, Yaya boss yaushe ka shigo?" "Ban dade ba, ina kwana?" Yace yana dauke kansa dga kallon yarinyar "Lafiya lou, baku tafi ba ashe." "Eh Baba be gama shiryawa ba, shine nace bari na shigo mu gaisa,wacece wannan Anty?" "Auw wai Jidda? Jiya na taho da ita yata ce, yar wana ce amma ta dawo hannu na da zama." "Ok."  Kawai yace yana tabe bakin sa, sai ya mike "Nima gobe zan koma in sha Allah, zan dade wannan karon har sai na kammala sannan zan dawo." "Wai, Masha Allah, zamuyi kewa. Allah ya bada saa da nasarar abinda aka je nema." "In sha Allah Amin." Yace yana ficewa, d'aga murya tayi tace masa a dawo lafiya ya amsa daga chan ya karasa ficewa. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107      [11/25, 3:54 PM] Rano2: *Sanadin*                *Labarina*                      Free Page (4) ©®_Hafsat Rano_ ** Tariq ne yake tuka motar Fauwaz na gefen sa,Baba a baya yana duba labarai a wayar sa jefi jefi suna hira da Fauwaz wanda shima rabin hankalin sa yana kan wayar sa yana duba wani pdf. Be fi sau biyu Tariq ya saka musu baki a hirar da suke ba har suka isa garin su Baban in da zasu dauko Hajiya Yaya A kasan wata bishiya yayi faking kannen Baban dake zazzaune suna shan inuwa suka mike dukka suka yo wajen motar. Fauwaz ne ya bude ma Baba kofa ya matsa baya ya fito, ya shiga mika musu hannu suna gaisawa, kananan kuma suka russuna suna gaishe shi. Cikin gidan suka dunguma suka shiga gaba daya, zuwa tsohon shashen Yayan kafin ta koma birni tun daga zuwa wani asibiti da tayi Baban yace tazo kenan, bata son birni sam amma babu yadda ta iya haka dai ta hakura bayan ya samu wasu daga cikin yan uwanta sun saka baki, duk da haka bata son zaman ta a cikin gidan sa dan ba wani shiri suke da Mama ba, ita Yaya dama bakin ta baya shiru bata gani bata tanka ba shiyasa tasu sam bata zo daya da Maman ba, tace Maman ta fiya isa da izza dan iyayenta wasu ne, shiyasa da Baba yazo mata da maganar auren Halima ta bada goyon baya dari bisa dari dan a ganin ta a lokacin ne zai auri daidai dashi. Hayaniyar Yayan suka fara ji tana ta fada da sababi, muryar ta a sama sosai ta dage tana fada bilhakki da gaskiya, murmushi Baba yayi, ya girgiza kansa yayi sallama a tsakar gidan, muryar sa ta sakata yin shiru ta amsa sallamar tana jefar da sandar da yake hannun ta. Fuskar Tariq a hade dan shi ba kasafai ya fiya son hayaniya da shiga cikin mutane ba duk da Baba yana tirsasa masa shiga cikin yan uwan sa dan suna da matukar yawa, yanayin sa ne a hakan kamar Safiyya, su suko yo Mama dan itama bata cika son mutane ba sai wanda tayi mugun sabo dashi. Shima kamar Maman ba shiri suke da Yayah ba, dan kullum yi masa korafi take bashi da sakin fuska, surutun ta shi yafi komai damun sa, dan idan ta fara magana baya jin ko hadiyar yawu tana yi. Fauwaz ne dan dakin ta da Amira, sune suka yo ta a surutu da kwashe kwashen mutane kowa nasu ne. Tabarma ta dauko zata shinfida musu fauwaz ya karba ya tayata, ta zauna a gefen gadon ta suka gaisa da Baban sannan su Fauwaz din suka gaishe ta ta amsa tana ficewa taje ta kawo musu ruwa ta ajiye sannan tace "Ashe zaku zo, na dauka fa sai wani satin wallahi, ban gama abubuwan da nake anan din ba." "Menene baki gama ba Yaya?" "Em.. em akwai wani biki na yar Hajara nan kasa damu, babu dadi ace ban tsaya an yi bikin dani ba." "Ayya, sai a basu hakuri Yaya, kinga fa lokacin komawar ki wajen likita yayi har yana neman wucewa." "A ah gaskia ba zaa basu hakuri ba, sai dai a bani gudunmawa me tsoka na bata, sai kuma ka aiko matar ka itama tazo ranar bikin da gudunmawar ta." Tace tana yin kicin-kicin da fuska, murmushi Baba yayi yace "An gama Yaya, sai kuma me?" "Shikenan, sai mu tafi tun da kayi niyya, ni wallahi dan ba yadda zan ne, a kai mutum a ajiye shi waje daya haba!" "Kiyi hakuri Yaya." "Idan ban hakuri ba ya zanyi toh? Fatan dayafi karfin ka ai sai ka mayar dashi wasa." Har Kawu Rabi'u ya kawo madara da kwan zabin da ya tafi karbo wa Baba bata daina sababi ba, magaanar ta kadai kake ji a dakin sai dai Baba yayi murmushi lokaci zuwa lokaci ya amsa mata, shi kam Tariq ji yake kamar ya fice amma yasan idan yayi haka zai gamu da fishin Baba, shiyasa ya hakura ya zauna kawai yana sauraron surutun ta wanda baki daya babu magaanar da za'a kama.    Fita Baba yayi yace zai je waje ya zauna da yan uwan sa kafin Yayan ta gama shiryawa, yana fita Tariq da ya tabbatar ya kule yaja tsaki yana dafe kansa. "Uwarka kake wa tsaki bani ba." Tace tana hararar sa, kallon ta yayi idanun sa na yin kasa sosai yace "Ni ba dake nake ba." "Ko ma da wa kake, mutum sai kuncin tsiya ba yar fara'a haba.". "Yaya Ya Tariq fa shine angon ki, ki dinga lallabashi." Fauwaz yace yana kokarin sake rura wutar fadan, buga cinyar ta, tayi tana daga murya "Allah ya kiyashe ni da aikin dana sani, na auri mutum irin wannan ai na kade har ganye na, matar sa ta shiga uku wallahi." "Idan kun gama ni ina waje." Yace yana mikewa, ta rakashi da Allah raka taki gona ya fice kawai ya bar Fauwaz yana kyalkyala dariya, da gaske dariya suke bashi musamman Tariq da ya kasa gane wasan Yayan irin wanda ake yi na tsakanin jika da kaka, da gaske yake daukar komai duk da ba kasafai ya fiya nuna fushin sa ba amma zaka ga sam baya sakewa da ire-iren wasannin.    Shi ya taimaka mata ta karasa hada kayan ta sannan ya daukar mata jakar, suka fito ta dinga shiga waje-waje tana musu sallama tun yana bin ta har ya gaji yace yana mota. A kwance ya samu Tariq din ya kwantr da kujerar side din me zaman banza fuskarsa rufe da hular da ya saka, booth ya bude ya saka kayan Yayan sannan ya dawo ta side dinsa yayi masa magana, mikewa yayi ya fita ya bashi wajen ya koma mazaunin driver. "Har yanzu ka kasa gane wace Yaya." "Haka aka ce maka?" "Ai naga kamar abun yana damunka, banda yawan maganar ta she's very nice and fun to be with, zatayi ta saka dariya ne." "Ni kuma sai aka ce maka dariya nake so nayi ko? Bani da aikin yi sai dariya ko?" "Ba haka nake nufi ba, yawwa gata nan ma ta fito, case closed." Yace ya ja bakin sa yayi shiru. "Ni zan bude kofar da kai ne kenan?" "Afwan Hajiya Yaya, wane mutum ya bar sarauniya da bude kofa?" Ya bude mata da sauri ya taimaka mata ta shiga, sannan ya rufe mata kofar. "Ranki ya dade." Yace yana dariya "Kafi oo sau dubu, Allah dai ya baka mata ta gari me hankali da sanin ya kamata kamar kai." "Amin." Yace yana cigaba da dariya, Baba ne yazo ya shiga motar kusa da Yaya, sannan suka sake sallama dasu Kawu Rabi'u, Tariq yaja motar suka fita daga kauyen. Gudu ya soma yi sosai bayan sun hau babban titi, salati Yaya ta fara yi tana salallami. "Tariq, rage speed din nan." Baba yace yana kokarin kwantar mata da hankali "Anya kalou yaran nan yake? Ba zaa kaishi ayi masa rukiya ba kuwa?" Tace bayan ya rage tafiyar sosai, ta cikin rear mirror ya kalle ta, ya maida kansa gaba ya cigaba da tukin sa yana jin Baba da Fauwaz suna dariya "Ba abin dariya bane wallahi, dole ma a nemo Malam Na Allah yayi masa rukiya gaskia." Yana jin su yayi musu shiru tukin sa kawai yake yana fatan su isa lafiya ya tattara ya bar garin gobe dan yasan tunda ta dawo ba zata kyale shi ba sam.    Har suka isa gida magana daya take, aikuwa yana gama parking yayi saurin fita ya dauki kayanta a booth yayi cikin gidan da sauri. Anty ce a bangaren Yayan tana karasa gyara mata sashen, ya dire jakar yana jan siririn tsaki. "Ya akayi?" Tace masa cike da kulawa "Kai na ke ciwo." "Kaje akwai panadol a kan fridge ka dauka ka sha, sannu." "Ok." Yace yayi saurin barin wajen dan baya so suzo su tadda shi, part din Antyn ya shiga, babu kowa a falon ya dauki paracetamol din ya nufi kitchen zai dau ruwa marar sanyi dan shi a rayuwar sa baya shan ruwan sanyi sai idan ana tsananin zafi.     Tana tsaye a jikin drawer din kitchen din tana gyaran kayan miya, kafarta ya kalla a ganta kamar kara, ya dauki ganin sa zuwa wuyanta da yayi masa kama da murkin lema, mamaki ya sake kamashi ganin tana aikin cike da kuzari, a yadda take da ramar nan be yi tunanin ko numfashi tana yin sa daidai ba, gani yake kamar ko kwakkwaran motsi tayi zata iya karyewa. Gyaran murya yayi ta juyo a tsorace, ya dauke ganin sa daga kanta ya dauki ruwan ya fice. ***Da gudun su suka fito jin sallamar Yayan, tana tsaye a tsakar gida suna gaisawa da Anty da su Abu, Amira ce ta rungumeta, tayi kamar zata yar da ita, ta tureta tana dariya "Ke baki san kin girma bane ba? Ko dan har yanzu baki fara kirgar dangi ba?" Kunyace duk ta kamasu, Anty tayi kamar zatayi dariya sai kawai tayi gaba tana cewa "Yaya muje ki huta karki biye musu." "Ai fa dan na kwaso gajiya, shima Alhaji ya rasa da wanda zai zo daukata sai da wanchan mahaukacin dan naki, ya dinga gudu dani duk yasa dan abincin da naci ya zazzage." "Wai Tariq?" "Kina da wani mahaukacin dan bayan shine?" "Yanayin sa ne haka Yaya." "Shi kansa wanda ya gado din haka muka sha fama dashi ya buga ya barni, idan zamu kwana be ce min ufffan ba, bana tanka masa haka akayi zaman nan." "Allah sarki, Allah yasa ya huta." Anty tace tana ajiye mata flask din ta da aka zuba mata kunu wanda ya zama kullum sai ta shashi, saboda sabo. "Kunu ne? Kai Allah yayi miki albarka kinji? Allah ya baki kema masu yi miki." "Amin." Tace tana murmushi, sai kuma ta fita ta bar Amira da Umaima da Yayan "Welcome back granny, we missed you.!" "Uwar granny din, na fada miki bana son sunan ko? Sai karyar turanci, toh turancin ma..." "Ba kyau zagi fa Yaya." "Anyi, idan ban yi ba ai ban cika bakatsiniyar ba, kuma ko gobe kika sake min turanci sai na zagi turancin, a banza a wofi wayon a zagi mutum ne." "Bari kiga, amira sai kin taho, ni nayi gaba, Allah ya dawo da mu ai." Ta mike, "Idan kin je karki dawo, yar nema kawai." "Almasifatu." Tace ta ruga da gudu, tashi Yayan tayi ta jefa mata pillow din kujera "Yar nema, zaki dawo har in da nake ne." ***Be shigo gidan ba sai wajen takwas na dare, lokacin Mama ta dawo, ya sameta a dakin ta, tana waya da kawarta, zama yayi akan bedside drawer ganin sa yasa ta katse wayar. "Tariq! Ta kira sunan sa, amsawa yayi yana kallon ta "Ya akayi?" Tace tana zama daga gefen gadon kusa dashi. Tun bayan da ya fara wayo halin sa ya fito sosai, babu wanda yake zama ya fadawa matsalar sa, ya sha yin ciwo a daki shi kadai babu wanda ya sani, baya taba cewa ayi masa abu sai dai ka fuskanta da kanka kayi masa amma ba wai dan ya tambaya ba, da farko halin sa ya fara tsorata ta, amma kuma kasancewar kakansa mahaifin Baban haka yake sak halin sa ya saka kawai ta hakura dan tasan biyu ce ta hadu ita kanta miskila ce. Ganin sa yanzu ya saka tasan akwai muhimmiyar magaanar da zai mata shiyasa ma ta katse wayar dan zai iya chanja shawara cikin kankanin lokaci. "Ina jinka." Ta sake maimaita masa tana kallon fuskar sa "Dama na gama hada kayan tafiyar ne, sakon da kika ce zaki taho dashi daga cikin gida." "Oh ai ban manta ba Tariq, gashi chan miko ledar chan, karfe nawa ne jirgin naka?" "9am, amma da asubah zamu fita." "Ok, Allah ya kaimu, ya bada sa'ar abinda aka je nema." "Amin." Yace yana rike da ledar, be koma ya zauna ba, hakan yasa ta gane dama abinda ya kawo shi kenan. "Nagode." Yace ya juya ya bar dakin, tayi murmushi kawai tana bin bayan sa da kallo. ***Da asubah bayan sun idar da sallah ya shigo cikin gidan, ya wuce shashen Anty ya kwankwasa, suna zaune bayan sun idar da sallah ita da Jidda suna karatun al'qur'ani, ta dauka Baba ne dan shine yake shigowa da asubah ya duba duk wadda ba ita ce da girki ba, tashi tayi ta bude kofar ganin Tariq yasa ta tuna da magaanar tafiyar sa "Ba dai har kun fito ba?" Tace tana matsa masa ya shigo ciki Kamshin turaren sa na Versace ne ya gauraye falon, ya zauna a kujerar dake gefen kofar sannan yace "Barka da Safiya Anty!" "Barka dai, ka tashi lafiya?" "Alhamdulillah, yanzu muke shirin fita, jirgin karfe tara ne." "Ayya, Allah ya kaiku lafiya ya tsare, ya bada sa'ar abinda aka je nema." "Amin ya Allah." Yace yana mikewa, "Ina kwana?" Ta gaishe shi cikin muryar ta da take kara sashi mamakin yanayin ta, hatta muryar ta kama take da yanayin jikin ta, yar firit muryarta kamar ana busa usur. Be amsa ba sarai kuma yaji sai da Anty tace ana gaishe ka sannan yace. "Lafiya." A gajarce, maimakon ya tafin sa kawai ya tsaya yana nazari, wajen minti daya ya dauka yana tsaye yana juya magaanar da take masa yawo akai, kafin yace "Anty ki kai yarinyar nan asibiti a duba ta, inaga bata da ishashiyar lafiya." "Jidda?" Gyada kansa yayi "Yes, baki ganta ba? Tayi rama da yawa kar ayi iska me karfi ta tafi da ita." Dariya sosai ya bawa Anty, ta dinga girgiza kanta cike da mamakin sa "Toh shikenan Tariq, zan kaita." Ajiyar zuciya ya sauke kamar wanda yayi wani aiki babba yace "Yawwa. Sai anjima." "Allah kaddara saduwar mu." Tace ya fice da sauri yana tuna lokacin da ya rage masa. [11/25, 3:54 PM] Rano2: *_Sanadin_*                *_Labari nah_*      Free Page ( 5) ©®Hafsat Rano ****Duk da karancin shekarun ta amma maganar sa tayi mata zafi, kuma tsakanin sa da Allah yake maganar, kamar ya kushe halittar ta ne ko wani abu, amma kuma da ta sake kallon kanta sai taga kuma akwai kamshin gaskiya a maganar sa, tabbas tana da rama ta ban mamaki, dan ita kanta wani lokacin sai ta dinga jin kamar zata karye. "Haka Tariq yake, yanzu akan wannan maganar asibitin ko yaje sai ya sake kira ya jaddada min, da gaske yake daukar ire-iren wadannan abubuwan musamman da ba wani saka baki ya cika yi a abu ba, amma duk abinda kuma ya damu dashi toh fa baya hakura sai ya cim masa." Shiru tayi bata ce komai ba har Antyn ta gama bayanin da ta lura so take ta wanke shi, tashi tayi kawai ta soma gyara falon ita kuma Anty ta nufi kitchen dan sama musu dan abinda zasu ci kafin hajiyar gidan ta kirasu zuwa karin kumallo dan duk ranar girkin ta sai an sha yunwa a gidan musamman yanzu da Baba zai fita da asubah ba dashi za'a karya ba dan yace daga airport din ma wani wajen zai yi suna da meeting na majlisun su a masallaci. ***Safiyya ce kawai ta fito da zai tafi ita da Mama suka rakashi har mota, dan su Amira ce musu yayi su zauna kar wadda ta fito baya son ire-iren wadannan abubuwan, last da zai tafi suka sha kukan su yana kallon su shi abun ma mamaki ya bashi, shiyasa wannan karon yace kar su fito, har ya shiga mota ya tuna da Yaya, shi shaf ya ma manta da ita, ya kuma san idan har ya tafi be mata sallama ba ya shiga uku, dan maganar ba zata taba karewa ba ta dinga mita kenan, fitowa yayi daga motar ya nufi bangaren ta yana fatan ya sameta ta koma bacci, yana tura kofar falon ya ganta tana shirin fitowa, da sauri yayi baya ta kalle shi "Na zata ai tafiya zakayi baka zo ba." "Ban tafi ba." Yace "Na zata ai nace, wajen ka nake shirin zuwa yanzu haka ma, zauna muyi magana." Tace tana zama, kamar kar ya zauna sai kuma ya zauna "Kana ji, nayi magana da wani malamin mu na chan kauye, yace zaa kawo maka rubutu kasha idan abun be sauki ba sai ayi maka rukiyya, bansan yau zaka tafi ba, ba wanda ya fada min sai da babanku ya dawo yake fada min, yanzu sai ku fara biyawa ku karba sai ku wuce." "Ina?" "Ban sani ba." "Allah ya baki hakuri, zamu biya mu karba." Yace ya mike "Karka fa tafi baka karba ba, ka kira su ayapot din kace su jira ka." "Toh, zan kira." "Yawwa, Allah ya baka lafiya kaji." "Amin." Ya amsa yayi saurin ficewa, ya san rigimar Yaya shiyasa shi duk abinda tace toh yake ce mata,in ba haka ba yaushe mutumin da zai yi tafiya, a jirgi ma ba a mota ba ace wai ya kira yace a jira shi, rigimar ta yawa ne da ita shi takamaimai ba me san rashin lafiyar me yake ba da har za'a ce ya sha magani. Yana zuwa ya fada mota, Baba ya fito suka tafi. *** Bayan tayi wanka suna zaune da Muhammad da Usman suna bata labarin ball Anty tace ta taso suje ta gaida Yaya, tashi tayi rike da hannun yaran suka fita zuwa bangaren Yayan da yake daga gefen gidan, tana dan madaidacin tsakar gidan ta, a zaune Abu na shanya mata kaya suna hira suka shigo. Da ido Yayan ta kafe Jiddan har suka karaso ta durkusa kasa ta gaishe ta, ta amsa a sake kafin ta dora "Ina kika samo yar fillo Halima?" "Yar gidan Yaya ce fa, Hauwa'u." "Allah sarki, itace ta girma haka." "Itace." "Lallai, amma dai ya bar miki ko? Dan banga amfanin zaman zankadediyar yarinya kamar wannan a hannun makirar matar nan ba Lami." Dariya tayi "Eh ya bar min."  Tace a kunyace "Kai madallah madallah, zumunci kenan, ya kyauta ke kuma Allah ya baki ikon rike ta da amana, ya baki ikon tarbiyarta." "Amin Yaya." "Kinga shikenan nima na samu yar daki, dan da alama zatafi zabiyoyin chan hankali. (Su Maryam)." Dariya kawai tayi, ita kuma Jidda tana rakube a gefen tabarmar tun shigowar su, su usman suka koma. Antyn ma cewa tayi tana zuwa ta fice ta barta a wajen Yayan dan bata so tace ta taso, tana fada Yaya zata hau sababi, shiyasa ma kawai tace mata kawai tana zuwa.    Suna zaune Yaya na ta faman bata labari, labarin rayuwar ta da dah, wani tayi dariya wani kuma sai tayi shiru musamman idan Yayan ta baro wani zancen da bata gane ba. Cikin hirar ne ta sako maganar Tariq, ta rage murya sosai sannan tace "Aljanu ne dashi fa, ina kyautata zaton aljanun kakansu ne suka dawo kansa, halin su daya da Maigidan nan, gashi naga alamun har so yake yafi Malam bakin hali (Mijinta)..." Sai ta dora tana sake rage murya "Kinsan fa tsabar bakin halin Malam, duk sanda na haihu sai ya tattara ya koma dakin zaure, ko dan ba zai gani ba, har sai mun yi arba'in, idan bako ya shigo gidan ba zai taba sanin yana nan ba, ko tarin sa ba zaki ji ba, kum bakin sa ko wari baya masa." "Allah sarki, yanayin sa ne a haka." "Ba wani ke, bakin hali ne kawai." Shiru tayi kawai dan bata san me kuma zata sake cewa Yayan ba,sauya labarin tayi zuwa wani daban sai ga Fauwaz ya shigo, ya kalli Yayan ya kalli Jidda sai kuma yayi murmushi "Yaya bakuwa kikayi ne?" "Toh baki abun magana an hallaro (wai Yaya ce take cewa wani baki abun magana)" "Bakuwa kikayi ne Hajiya Yaya?" "Ba bakuwa bace, kwanan ta nawa a gidan nan baku hadu ba?" "A ah, kinsan mu idan ba abu ba, ba kasafai muke shiga cikin gidan ba." "Toh gata nan, kanwar kace dan ta zama yar gidan nan itama, yar Yayan Halima ce." "Toh Masha Allah, sannun ki." "Ina wuni?" Tace tana mikewa "Lafiya lou, kina lafiya?" Shiru tayi tana wasa da hannun ta "Zaka korar min ita daga zuwa, Jidda yi zamanki mu cigaba da hirar mu." "Ah hira kuke? Jidda zauna ayi dani nima." Sai ya zauna a wajen da ta tashi yana tankwashe kafarsa, "Zan je na taya Anty aiki." "Kin jiki, yar kumamar nan dake wane aiki zaki iya?" Yaya tace tana kallon ta Murmushi ta yi, Fauwaz yace "Ai ba anan take ba Yaya, sai tafi yaran chan aiki." "Tunda dama su ba uwar da suke tsinanawa ba, ayi magana ace boko, bokon banza bokon wofi." Dariya sukayi shi da Jiddan, Yayan ta cigaba da sababi akan bokon, sai ga su sun shigo part din, Amira ce ta ja hannun Jiddan ta zaunar da ita a gefen Ya Fauwaz, maryam ta tsaya daga tsaye tace "Tun muna daki muke jiyo maganar ki Yaya." "Ko kice daga bangon duniya ba." "A'ah dakin dai, kina magana ko hadiyar yawu bakya yi Yaya, ki dinga hutawa." "Tunda ki kike ci dani kike sha dani, ai sai ki gindaya min sharadi, mutum da bakin sa an isa a hana shi magana ne." "Allah ya huci zuciyarki gimbiya Yaya, ba abin fada bane." Tace tana zama a kusa da Amira, suka saka Yayan a tsakiya, wani iri Jiddah take ji, musamman da bata taba experiencing irin wannan rayuwar ba, sai take jin wata nutsuwa na saukar mata, a kalla zatayi rayuwa irin wadda mutane da yawa suke yi, a kalla zata san dadin zama cikin mutane tayi gogagya dasu cikin rayuwa.    Sun dade a wajen Yayan har sai da Mama ta aiko su zo kitchen lokacin girkin rana yayi, bata bi su kitchen din ba, ta wuce ciki ta samu Anty tana bacci ita da Usman , sai ta shige daki ta kwanta kawai tayi lamo akan gadon rayuwar ta na dawo mata daki -daki, mataki-mataki. Bata san daga nan wanne mataki zata taka ba, Amma ko ma wanne iri ne zatayi kokari wajen kula da rayuwar ta da kanta, dan ba zata so ta sake maimaita rayuwar ta, ta baya ba.     Washegari litinin suka tashi da shirin zuwa makaranta, tun asubah kowa na gidan ya mike aka hau shirin shiryawa, tana shara Anty tace ta ajiye taje tayi wanka dan tare da ita zaa tafi makarantar, fuskarta ce ta fadada da fara'ah, tayi saurin karasa sharar yayi wanka a gurguje dadi na kamata, kaya ta tarar akan gadon da skirt underwear sai half vest da kayan da Antyn ta bayar aka dinka mata, underwears din kuma Abu ta bawa ta siyo mata a kasuwa. Dauka tayi ta saka, ta shafa mai sannan ta zura sabon Hijab din da yake gefen kayan, tamkar ba ita ba, ta sauya sosai kayan sun mata kyau yar fuskar ta fayau ta sake fitowa. Hijab din da ya kasance mint green ya karbi fatarta sosai kasancewar ta fara sosai. Tana ta kallon kanta a mudubi Anty ta shigo tace ta fito su yi breakfast,  sai ta tsaya tana kallon ta baki bude "Masha Allah Jidda, kin yi kyau tabarakallah Masha Allah. Kin ganki kuwa? Lallai zaa yi kallon yan matacci anan." Murmushi tayi ta sunne kanta cike da kunyar yabon da Antyn tayi mata, tabi bayanta, ta bata tea da bread anan falon ta, tana sha Amira ta leko tace ta fito, ta tashi da sauri bata gama ba ta ajiye kofin, ta saka takalmin da Antyn ta bata, tace "Zamu tafi.." "Toh Jidda, Allah ya bada sa'a, kiyi karatu sosai kinji? Shine gatanki." Da kai ta amsa, ta nufi kofar ta biyo ta suka fito harabar gidan, Safiyya na tsaye rike da hannun Usman da Muhammad, ita tayi candy wannan shekarar, ta kalli Jiddan da suke fitowa tare da Amira rike da hannun juna, kauda kai tayi kawai bata ce komai ba, ta taimakawa yaran suke shiga motar, Maryam na ciki a zaune da Umaima, sai ga Fauwaz ya fito daga wajen su yana gyara hular da ya dora akan manyan kayan da ya saka, ya gaida Antyn sannan ya shiga gaba gefen me zaman banza. Zama Amira tayi bayan ta matsawa Jiddan itama ta zauna, driver da Baban ya samo musu saboda zuwa makaranta ya tada motar, suka fita daga gidan. Sai a sannan Safiyya ta gaida Antyn a gajarce ta shige ciki da sauri. Duk cikin yaran gidan Safiyya ce kawai bata sakewa da ita, ta kuma san dalilin yanayin da mahaifiyarta ta karbe ta ne, tana kokarin taya mahaifiyar ta kishi, shiyasa ma bata taba damuwa da yanayin yarinyar ba, sau tari tana ganin ta amma kallon kirki bata isheta ba bare ta samu matsayin gaisuwa. Tana shigowa falon sukayi kicibis da Mama, wadda ta cika tayi fam daga gani a cikin bacin rai take. "Ina kwana Maman Fauwaz?" "Bana son abinda kike min gaskiya, yanzu tsakani da Allah aure min mijin da kikayi be isheki ba, sai kin kakaba masa rike miki yar dan uwan da ya kasa rike amanar da Allah ya bashi, ba zaki duba shi nauyin da yake kansa ba na yaran sa." "Me ya faru?" Tace kamar bata san maganar da Maman take yi ba "Makarantar yaran nan da kika saka babansu ya kai yarinyar da kika dauko." "Wai Jidda?" Shiru tayi ranta idan yayi dubu ya baci "Ayya kiyi hakuri, shi da kansa yayi niyya yace zai saka ta bani na nema ba, sannan naga ai d'a na kowa ne Maman Fauwaz, ba'a san wanda zai more shi ba." Tana fadan haka ta shige ciki da sauri dan tasan tsaf yadda ran Maman yake a bace za'a iya yin batacciya. Bata san tashin hankali ko kadan shiyasa duk yadda taso suyi rigima taki bata kofa, idan ta fara ma sai tayi shigewarta daki ta barta. ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/25, 3:54 PM] Rano2: *__SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (6) ****Fauwaz ne yayi mata duk cike-ciken da ya kamata yayi mata, ya biya kudin da komai sannan akayi mata interview, yanayin karatun ta ba irin nasu bane dan haka abubuwa da yawa bata gane ba, a jss 2 head teacher din yace a sakata Fauwaz ya roki a sata 3 tunda yanzu aka juya session din, hoping zatayi coping kafin time din, haka akayi aka sata ya rakata har kofar class din su da yake kusa da na su Amira ss1, tsayawa tayi tana kallon sa, a hankali tace "Nagode Ya Fauwaz." Murmushi yayi mata sannan ya tafi, ita kuma ta shiga cikin ajin. Duk suka zuba mata ido suna kallon ta, tsayawa tayi daga jikin kofar ta sunkuyar da kanta kasa, Safeera ce ta taso daga seat dinta tazo ta sameta a tsaye tace "Taho ki zauna." Bin ta tayi zuwa seat din dake kusa da na Safeeran ta zauna sannan tayi mata godiya. "Nagode." "Ba komai, ya sunan ki?" "Jidda..." "Nice name, ni kuma sunana Safeera, ki saki jikinki, duk wadda ta raina miki hankali ki fada min." Murmushi tayi mata bata ce komai ba, uncle ya shigo suka maida hankalin su zuwa kansa, kowa ya mike aka gaishe shi sannan yace new comer ta tashi tayi introducing kanta, bata motsa ba dan da turanci yayi maganar sai da Safeerah ta rada mata, ta tashi da sauri a kunyace ta tsaya,ya sake maimaitawa "What is your name?" Tace "Jidda." "Hauwa'u right?" Ta daga kanta "Ki fada har da sunan Baba." Safeera ta sake whispering mata "Hauwa'u Ibrahim." "Ok welcome to Jss 3 Hauwa'u, seat down." Zama tayi jikinta a sanyaye, turancin shine babbar matsalar ta a yanzu, dan su a chan da Hausa ake koya musu yawancin subjects din. Introducing new topic yayi ya shiga bayani wanda kusan rabi babu abinda ta fuskanta, Safeera na lura da ita, har ya gama ya fita, ta kalleta bayan malamin ya fita tace "Baki gane ba ko?" Daga mata kai tayi alamar eh "Zan miki bayani idan an fita break, sannan karki ji tsoro, turancin ma bashi da wahala, da kin gane shikenan." "Nagode." Tace tana mata murmushi "Can we be friends?" Tace tana mika mata hannu, hannun ta kalla hakan ya saka Safeera yin dariya "Zamu zama kawaye?" Ta fada mata da hausa, gid'a mata kai tayi ta mika mata hannun itama, suka gaisa "Friends for ever." Tace tana sake matsar da chair din ta kusa da ta Jiddan. "Duk abinda baki gane da turanci ba ki fada min, sannan akwai dictionary ma, duk kalmar da kika ji baki gane ba, ki duba zaki ganta da meaning da komai, zakiyi mamaki yadda zaki improving sosai." *Shikenan, nagode sosai." Hannu ta mika mata "Taso muje muyi break kafin a dawo class." Mika mata hannun tayi suka fito compound din makarantar, Amira da ke zaune tare da friends dinta ta taso da sauri "Jidda." "Kin santa?" Safeera ta tambaya "Gidanmu daya." Amira tace sannan taja hannun ta "Muje kafin a koma class." Bin ta tayi safeera tayi tsaye tana kallon su, Asiya ce tazo kusa da ita tayi dariya tace "Daga ganin yarinya kin makale mata, gashi nan ai." "Ina ruwan ki?" Tace tana barin wajen, taje ta siya egg rolls guda biyu da lemon cway ta ci daya ta dauki daya ta je wajen da suke zaune da amira da kawayenta, ta mika mata "Kawata gashi." "Ta gode taci meat pie." Amira tace tun kafin ma Jiddan tayi magana, ran safeera be yi mata dadi ba, ta juya zata bar wajen Jiddan ta mike da sauri ta ce "Amira bari muje aji zan karasa rubutu." "Tsayani." Tace da sauri tabi bayan ta, hakan ya sakata sakin fuskar ta suka koma ajin suka zauna, ta karbi eggroll din taci kadan, ta ajiye sauran. Tun daga ranar Safeera ta zama kawarta, duk da da farko bata sake da ita ba, sai da ta fara fuskantar ta da halin ta, she's very simple ba kamar sauran yan ajin nasu ba, dan ba kasafai suke mata magana ba ma musamman tunda suka gano bata iya turanci ba. Dan ma suna shakkar Safeeran ne da wani abun ba haka ba, ita take koya mata duk wani abu da tasan zai saka yan ajin su kalli Jiddan a matsayin koma baya ko kuma ba level din su bace ita     Sosai ta bada himma akan karatun ta, duk kuwa da tana shan bakar wahala amma haka ta dage, ko yaushe ta zauna tana rike da littafi, babu maraya sai rago, kuma babu abinda ba zaka iya ba in dai ka saka ranka.    Rabin rayuwar ta a bangaren Yaya take yin ta, hakan yasa Amira da Maryam suma ko da yaushe suna shashen, bata bin su wajen su saboda ko taje ma bata samun fuska a wajen Maman dan kiri-kiri take nuna mata bata son ta tare da yaranta, sanin haka yasa itama ta tsaya iyakar matsayin ta, bata zak'e ba bare a samu matsala.    Tsakanin ta da yaran gidan musamman Fauwaz,amira da Maryam ba zata ce akwai wani banbanci da suke nuna mata ba, zuwan ta ma ya kara musu shakuwa da Anty tunda ko yaushe suna manne da ita idan basa wajen Yaya toh suna part din Antyn.     Bangaren islamiyya ma alhamdulillah, da naci da dagiya tana gane komai a hankali a hankali kan nata yake sake budewa, tun bata ganewa har ya zamana ta soma dauka sosai fiye da yadda tayi tunani. Hakan yake karawa Anty Jin dadi dan tana kyautata zaton ilmin shine gatan Jiddan ba komai ba. Aikin gida duk ta hanata komai girki kawai take tayata shima saboda bata so a samu matsala ko gaba idan tayi aure.    Sau kusan uku Tariq na kiranta bayan tafiyar sa, idan suka gaisa sai yayi mata maganar Jiddan duk da baya fadin sunan ta sai dai yayi alamar yadda zata gane, dariya kawai takeyi tace toh zaa yi, sau daya ta bawa Jiddan labari da ta ga bata nuna interest dinta akan maganar ba sai kawai ta share itama.    ***Rayuwa ta cigaba da garawa cikin ikon Allah Jidda ta kammala jss 3 zata tafi ss1, Amira Ss2, Maryam ss3 ita da Umaima. Hutu Anty ta shirya musu zuwa chan garin su, ta fadawa Baba yace idan sun shirya zai saka driver ya kaisu amma kwana uku kawai zasuyi su dawo. Shiru tayi dan taso ace ko sati ne su yi, kallon ta yayi yaga kamar tana tunani yace "Akwai wani abun ne?" "Eh wai da ko sati ne." "Kwana uku nace, ba kari kuma." "Toh Jiddah ko zaa barta ita tayi satin saboda Yaya." Da sauri ya waigo dan da har yayi shirin shigewa dakin sa "Ban gane ba, an yi hutun islamiyya ne?" " A'ah." "Toh kwana uku zakuyi ku juya, ni ne uban Jidda ni nake da iko da ita a yanzu ba Yaya ba, idan kuma iyakata zaa nuna min toh." "Allah ya baka hakuri."  Tace tana sauke kanta a kasa, daki ya shige be sake magana ba, Mama dake tsaye tun dazu a kofa tayi tsaki ta shigo fuskarta a hade, ta kalle ta itama ta kalle ta, ta sake jan wani tsakin sannan tace "Ki gama munafuncin ki da shishigin ki da son lallai sai kin nana masa yar da ba tasa ba, zaki wani fake da munafunci da iyayi." Tashi tayi kawai tayi hanyar fita ta bar mata dakin, dan dama basa taba hada zama waje daya dan in dai tana wajen Baba baya ko kallon Antyn sai itace ma zata dinga kokarin sako ta a hirar su irin na kissar nan,shiyasa ta shafawa kanta lafiya take iyakar kokari wajen gujewa abinda zai dagula mata sukuni. ***A falon ta, ta same su Amira na karanta musu wani story book, Adil ne akan kafar Jiddan, Maryam kuma na ta saman kujerar tana mata tsifa, wajen kwana biyu kenan Aunty tana fama da ita akan tsifa dan da gaske ta tsani abinda zai sata taba gashin ta, shiyasa tsifa ke mata wuya sosai. Su kuma tsawon gashin nata ne yake birgesu dan ranar da ta fara bude kanta Amira da Maryam tamkar zasu lashe ta, suka dinga tabawa suna dama sune da an ga gayu, ita dai murmushi kawai takeyi dan ita be wani dadata da kasa ba. Duk sati ake basu hairstyle a school shiyasa ma take yin kitson amma shima dan ba yadda zatayi ne seniors din nan ba mutunci ne dasu ba. Satin da aka soma exams kuwa ba'a basu hairstyle din ba shiyasa ta barshi har sai da Anty tayi magana.    "Tsifar kike tayata Maryam?" Anty tace tana zama daga kujerar dake daura da kofar shigowa part din nata dan fita zata kuma yi, "Wai bata son tabashi, shine nace ta kawo nayi mata. Nice nake da gashin Jiddah tab, Ai da an ga gayu wallahi, bama fa shi da wahalar tsifar saboda laushin sa" "Lallai kam, kin taimaka mata. Idan kun gama Jiddah ki hada kayanki wanda zamu tafi dasu, na fadawa Baba yace kwana uku kawai zamuyi amma." Tashi tayi tsaye da sauri cikin tsananin jin dadi tace "Wayyo zan je naga baffanah, yaushe zamu tafi?" "Gobe da safe in sha Allah, ki duba abinda bashi da wanki ki wanke." Murna ta hau yi, fuskarta ta gaza boye farin cikin da take ciki, dariya suka dinga mata, Amira ta kalli Anty tace "Anty dan Allah zan rakaku." "Na'am?" Sai kuma tayi shiru dan tasan ba lallai uwarta ta barta ba, ba kuma dadi tace wa yarinyar a ah, shirun ta ya saka Amiran ta zata ko ba zata da ita bane "Dan Allah Anty." "Ba k'i nayi ba Amira, amma ki tambayi Mama idan ta barki shikenan sai mu tafi." "Nima zan je." Muhammad yace ashe suna jin abinda ake cewa, "Nima." Usman ya fada yana mikewa yazo wajen Antyn, sai Muhammad din ma ya tashi suka tsaya mata a gaba "Shikenan toh duk zani daku." "Yeeeh yeeeh." Suka hau tsallen murna, murmushi kawai Anty take cike da jin dadi, a kalla zuwan Jidda ya kara mata shakuwa da yaran sosai. Duk da tasan ba lallai Maman ta bar su ba, amma ko a hakan ita taji dadi sosai ba kadan ba.    Tunanin yadda Amira zata fadawa Mama takeyi gashi har ga Allah tana son zuwa taga yadda garin yake da labarin da Jiddah take basu. "Idan na fadawa Mama zata yarda?" Ta tambayi Maryam, dage kafada tayi alamar oho sannan tace "Kema kinsan wace Mama, da hakura kawai kikayi." "Ba zan hakura ba, i will try my luck." "Allah ya bada sa'a toh." Tace tana mikewa "Bari kiga naje na aro wayar Ya Safiyya nayi game." "Tab! Allah sa ta baki." "Zata bani ai tasan nima an kusa siya min tawa." "Sai dai haka, moha taso ka rakani wajen Mama kaji, Allah yasa ta bar mu." Rike hannun sa tayi suka nufi bangaren Baba da suka san zasu samu Maman achan, kuma tasan in dai Baba yace yes Mama ba zata hana ba sai dai zata sha rakwashi da kallon banza, duk wannan daga baya ne in dai har sun tafi. Sallama tayi daga kofar Muhammad ya kwace hannun sa ya shige ciki ita kuma ta tsaya tana jira a bata izinin shiga. "Uwata shigo mana." Baba yace yana gishingid'e yana duba wayar sa, shiga tayi kanta a kasa gabanta na dukan uku uku, ta ki yarda ta hada ido da Mama kwata-kwata, ta zauna a gaban Baban sannan tace "Em em dama." "Dama me? Ina jinki." "In dai kaga Amira na haka ai akwai abinda zata tambaya." "Ina jin ki toh." "Dama Baba, so nake na bi Anty nima." Da sauri Mama ta ajiye abun hannun ta, ta kalli Amiran da kanta yake kasa, ranta yayi masifar baci, ta kalli fuskar Baban ta karanci yanayin sa, fuskar sa a sake yana shirin yin magana ta rigashi "Kin manta da bikin ummul? Ko ba zaki ba?" "Wannan satin ne bikin?" Baba ya tambaya yana kallon Maman "Eh wannan ne, har sun yi anko ma fa, inaga dai ta manta,ummul ba zata ji dadi ba idan baki je ba." "Ummul ba sa'ar Maryam bace ba? Ko Safiyya ma, ba komai sun wakilci uwata, ki shirya ki bisu kinji." "Nagode Baba, Allah ya saka da alkhairi." Sai ta tashi da sauri ta fita, ba tare da ta hada ido da Maman ba, tana fita Muhammad ma yace zai je, shima Baban yace toh. Kasa karasa abinda Maman take tayi a dakin, ta fice da sauri dan idan ta zauna ba zata iya rike bacin ranta ba. [11/25, 3:54 PM] Rano2:             SL         *7* ©®Hafsat Rano ****A tsakiyar falon ta tsaya ta shiga kwalawa Amiran kira, a tunanin ta, tana cikin wajen Antyn, bata san direct wajen Yaya ta gudu ba dan tasan haduwar su ba zatayi kyau ba, shiyasa ta salallaba ta gudu, ba kuma zata yarda su hadu ba sai gobe , dan duk bala'in Yaya sai dai ta barta amma a wajenta zata kwana ta san kuma Mama ba zata taba biyo ta wajen Yayan ba,gaisuwa safe ce kawai take hada su kuma shima kwana biyun nan da daminar ta dan ja baya zafi ya sako kai tsakar gida take fitowa tun sassafe ta basa baza tabarma.     Dakin ta, ta shige ta san duk daren dadewa zata zo ta sameta ne, bata amince ba babu in da zata bi Halima dan har yanzu bata gama yarda da ita ba, duk yaron da zaka dauke shi aiki karshe ya aure maka miji ba kuma zaka taba amince masa ba har duniya ta nade, duk da idan da zaa saka mata wuka ace ta fadi aibun ta ba zata ce gashi ba, amma ita sam bata amince da ita ba, ba kuma zata fara daga yanzu ba, ta bar yarta ta bita garin da bata san me zata tarar a chan ba.     Da la'asar fita ta kamata, ta shirya ta fice daga gidan ta manta shaf da batun Amiran, shagon ta ne aka kawo kaya, abinda ya fitar da ita kenan tare da Fauwaz, wanda basu suka shigo gidan ba sai dare. Kasancewar a gajiya ta dawo bata bi ta kan ta ba, ta kwanta dan da wuri zata sake fita washegari akan ragowar kayan da basu riga sun iso ba.    Shirin su suke hankali kwance, murna wajen Jidda da Amira baa magana, Maryam a kasan ranta tana son bin su Amma bata shiryawa fadan Mama ba, shiyasa kawai ta hakura tana kallon su. Kitso akayi ma Jiddan me kyau duk da tsananin santsin gashin kanta amma da ya hadu da bahijja me kitso sai gashi ta kama mata shi, yayi kyau sosai dan sai da taji kunya yadda su maryam suka dinga koda ta wai kamar kan larabawa. Cikin dare ta kasa bacci saboda zumudin tafiyar ana kiran sallah ta mike kamar wadda aka tasa, ta hau shiryawa tana sake hade kayan da zata tafi dasu. Tun dare dama tayi shara saboda haka babu datti, sai yan kayan da ba zaa rasa ba suma ta tattare kowanne ta saka shi a in da ya dace. A haka Anty ta sameta, batayi mamaki ba dan idan da sabo ta saba da wannan, sam Jiddan bata da son jiki kuma duk abinda ta san ya kamata yi kawai take ba sai an ce ba, bare kuma yau da take da zumudin ganin baffanta. "Sannu Jiddah, Allah dai yasa kin yi bacci?" "Nayi." Tace sai kuma ta dan russuna tace "Ina kwana Aunty?" "Lafiya lou Jidda, bari na dora mana ruwan wanka dan da wuri zamu fita in sha Allah, idan kin gama kije ki ga Amira ko ta tashi." "Toh..." Tace cike da zumudi ta karasa abinda take ta nufi wajen Yayan dan Amira ta fada mata anan zata kwana saboda Mama.    Ta tashi har tayi sallah ma,amma kuma yanayin ta be nuna wa Jiddah tana cikin walwala ba, kallon fuskar ta tayi, sai kuma ta zauna a gefenta tana mata kallo me dauke da alamar tambaya "Na fasa zuwa." Tace a cikin yanayin da yake nuna kusa take da ta fashe da kuka "Mama?" Ta tambaye ta Daga mata kai tayi alamar eh "Ok kiyi hakuri." "Dan Allah mene dan na biku? Gaba daya Mama bata so taga muna harka daku bansan me yasa ba, yanzu ta turo Safiyya wai kar na soma bin ku." "Bakin kishin ta na tsiya ai bazai barta ta hakurar wa zuciyar ta, ta karbi abinda Allah ya riga ya kaddara ba." Yayah tayi maganar tana shigowa dakin rike da charbi a hannun ta, duk suka kalleta sai ta dora "Nace dai duk ba akan kishi ake wannan abun ba? Idan akan shi ne yaci ace an ajiya ko? Shekarar Halima kusan takwas a gidan nan harda arzikin Usman, idan hakan be zama ishara ba sai yaushe?" "Ba haka bane Yaya, tace wai bamu saba zuwa irin wajejen ba." "Uwarki ce bazan hanaki kareta ai, me zai sameku a chan da ba zai same ku anan ba? Kin taba ganin an yi wa Allah wayo? Ba hujja bace bakin kishi ne kawai." Mikewa Amiran tayi tana jin babu dadi, bata son maganganu irin haka akan Maman, musamman daga wajen Yayah, a kullum so take taga komai ya zama normal Mama ta yi hakuri ta bar komai ya wuce "Idan kun gama shiryawa zan shigo." Ta wuce kawai ta bar part din ranta duk babu dadi "Yarinyar nan ba dai hankali ba dan tafi uwarta wallahi, dama uban yan girman kan chan da safiya sune suka yo uwarsu, amma sauran ba ruwan su." "Uhum." Jidda tace itama ta mike, tafice ta bar Yaya na cigaba da mitar zancen. A gurguje tayi ma Usman wanka tayi nata ta shirya cikin riga doguwa ta atamfa ta sallah da Baba yayi musu ita da Maryam da Amira. A shirye ta samu Aunty tana zaune tana waya a gefen gadon ta, yadda take wayar ya tabbatar mata da Baffa ne, zumudin ta ne ya karu sanda taji Antyn tana cewa sai sun zo. Bayan ta gama wayar ne ta dauko mata sarka da dankunne me kyau ta bata ta saka sannan tace ta jirata a falo. Fita tayi ita kuma ta yafa mayafin ta ta nufi sashen Baban, ta same shi ya shirya shima, da mamaki take kallon sa "Ba dai fita zakayi?" Tace tun daga kofa, kafin ya bata amsa Mama ta turo kofar ta shigo, ya kalle ta sannan ya maida kallon sa wajen Auntyn yace "Tare zamu, inaso zan ga Yaya." "Yaran sun shirya?" Yace yana kallon Mama, dan dam tayi amma sai ta kame tace "Sun kuma chanja shawara kasan abun yara." Gid'a kansa yayi yace "Taimaka min da hula ta akan bedside Halima." "Toh." Tace ta wuce ciki, yana ganin ta shiga ya maida kallon sa kan Mama yace "Minti goma sha biyar na basu su shirya, Muhammad ma yace min zaije dan haka kar abata min lokaci." Wani kallo tayi masa, ya daga mata kai alamar haka yace, bata ce masa komai ba ta juya ta fice daga shashen. Dakin su Amiran ta wuce ta sameta a kwance a gado ta lulluba da bargo ranta babu dadi, a kanta ta tsaya fuskar ta a hade tace "Sai ki tashi ki shirya yana jiranku, saura ki tsaya bata lokaci yace ni na hana kuma." Da sauri ta mike zaune, tana kallon fuskar Maman cike da zumudin murna "Ki shirya Muhammad ma, ki daukar masa sababbin kayan sa." Daga haka ta juya ta bar dakin, da sauri Amira ta tashi ta hau ciro kayan ta a wardrobe da ta maida su, ta saka a trolley taje dakin Maman ta dauko na Muhammad ta hada, sannan ta shiga wanka ta watsa da mugun sauri sannan ta fito ta zura kayan ko shafa mai batayi ba,ta fita zata kira Muhammad Maryam tace mata ta masa wanka har ya tafi falon Baba, komawa tayi daki da sauri ta gyara fuskar ta, ta daura dankwali sannan ta dauko kayan nasu ta fito.   Babbar motar Baban ce da ake amfani da ita idan za'a je kauye ko wani waje tare, driver ne yake tukata sai Baban a gefen sa, kujerar baya jidda da amira suka zauna Anty kuma ta zauna a ta tsakiya ita da Muhammad da Usman, maryam kamar zatayi kuka da ta rakosu dan dai kawai bata son fushin Mama ne amma da itama sai taje, ita da Safiyya kawai suka rage a gidan dan Mama ta sake fita da Ya Fauwaz da Umaima tun dazu kuma kila sai yamma likis zasu dawo.    Hanya suka dauka sosai bayan an tsaya an yi siyayyar abubuwan da zasu tafi dashi. Tafiya sukayi a hankali har suka isa, hakan ya kara zumudin jidda ganin an dauku hanyar gidan, ta zura hannunta ta window tana feeling sanyayyiyar iskar dake kadawa. Parking Baba Driver yayi a kofar gidan dan ba wannan ne karon farko na zuwan sa da Baba ba. Baffa na jin tsayuwar mota ya fito da sauri suka yi kicibis a waje. Fuskar sa tamkar gonar auduga, idanun sa suka hango masa Jiddan sa, wadda ta sauya masa tayi haske ta dan yi kiba kadan, wajen Baba ya nufa kai tsaye duk da dokin ganin Jiddan, suka shiga gaisawa da tambayar bayan saduwa,cikin gidan suka dunguma suka shiga gaba daya, akayi sa'a Lami bata nan tayi tafiya zata kuma kwana biyu, gidan a share yake tas tas, sai katuwar tabarmar da Baffa ya shinfida a tsakar gidan, suka zauna dukkan su aka shiga gaishe gaishe. Duk da zumudi da son ganin baffan nata amma sai ta makale a gefe cike da kunya, takasa cewa komai. Dariya duk ta basu Baba ya tsokane ta akayi dariya kafin ta gaida Baffan ya amsa sannan Amira ma ta gaishe shi.    Wajen awa biyu Baba sukayi, suka sha fura da nono sannan suka ci dambu da Innar su Saude ta aiko musu, sannan suka shirya komawa shi da Baba driver, Kwan zabi Baffa ya basu masu yawa ya rakasu har mota Baba ya dauko kudi ya bawa Baffan ya karba da kyar yayi godiya. Ya bude masa kofar ya shiga ya sauke glass din yace "Yaya zan shiga siyasa in sha Allah, a tayamu da addua." "Kai Masha Allah, Alhaji ai dama irin ku ake so a siyasar kasar nan,ka chanchanta" "Kayya, zamu dai gwada jarrabawa mu gani." "Toh Allah ya taimaka ya bada sa'a." "Amin." Suka sake sallama suka tafi Shi kuma ya koma cikin gidan, ya samu Anty a zaune suka shiga hirar yaushe gamo, ya dinga yi mata godiya akan jidda sannan ya bata labarin zuwan da Baba yayi aka kaishi wajen likatan kashi tun daga lokacin ya samu saukin kafar dan har gona zuwa yake. Ita bata ma san anyi ba,dan be fada ba, kuma dama tasan ba fada din zai yi ba, haka yake ko yayi abu baya so a yaba masa yafi son kawai a yi shiru. ***Kwanan su biyu sosai Amira taji dadin garin, yanayin weather din yayi mata ga fura da nono abinda take matukar so kenan, gobe zasu tafi shima da kyar Baba ya kara musu kwana daya,dan be samu me zuwa dauko su bane ba ma shiyasa, kanya suke je tare da Saude suka samo suka zauna a tsakar gidan su Sauden suna sha tana basu labarin abun dariya, tashi Jidda tayi ta ce zata dauko abu a gida ta dawo. Gidan su ta shiga ta tarar da Anty zata fita hankalin ta a tashe, da sauri tace mata. "Jidda Muhammad yana wajen ku ne?" Da sauri ta girgiza kanta "A ah, tare muka bar su da Usman suna zaune." "Na shiga uku!" Tace tana yin gaba, da sauri jidda tabi bayan ta, suka hau neman sa, abu kamar wasa sai gashi an neme sa an rasa, iya kar tashin hankali Anty ta shiga. Sauran makota ne suka fito aka bazama nema, Usman dai yace yabi su Yaya Amira da Yaya jidda da suka fita, lokacin Anty tana sallah, su kuma sun ce be biyo su ba, kuka wiwi Anty take tana jin kamr ta hadiyi zuciya ta mutu, wannan wanne irin tashin hankali ne, ina ya shiga? Me zai faru? Yaya Mama zata ji idan wani abu ya same shi bayan da kyar ta yarda suka biyo ta, zata taba fita idan wani abu ya same shi? Ba zata fita ba ko a wajen mutane balle mahaifiyar sa. Har duhun magriba ya soma babu shi babu labarin sa, dukkan su kuka suke har Jidda da Amira da ta cika da tsoron abinnda zai faru da Muhammad din. ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/25, 3:54 PM] Rano2: *__SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (8) ****Kasancewar karamin gari ya saka suke da yakinin ba zai bata a cikin sa ba, sai dai tabbas ana kyautata zaton ba lafiya ba, daga chan gaban gidan su Jiddan akwai wata babbar rijiya, da duk mazauna wajen suke amfani da ita. Kamar an tsikari Aunty haka ta mike da sauri duk suma suke mike "A duba rijiyar nan, Allah ubangiji yasa ba fadawa yayi ba." Ta fashe da kuka, jikinta na rawa sosai tamkar mazari, Baffa ne da Baffan su Saude da wasu maza biyu suka nufi rijiyar dan duk ciki babu wanda ya yi tunanin dubawar. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Kalmar da aunty ta iya ji kenan daga bakin Baffa sanda ya leka kansa cikin rijiyar, saboda tsabar kaduwa ta yanke jiki ta fadi cikin wani irin yanayi. Nan da nan wajen ya cika makil da mutane aka samo masu shiga rijiya mutum hudu biyu suka shiga suka dauko shi, cikin yanayin firgici. ***Wani irin kuka aunty take, duk rashin imanin ka sai ka tausaya mata, Jidda da Amira ma sun ci kuka sun gode Allah, suna nannade a zaune gefen Aunty Usman na jikin Amira yana kuka shima duk da kukan be san na menene ba, waya Baffa ya dauka ya kira Baba, ya koma gefe ya sanar dashi abinda yake faruwa cikin yanayin dauriya dan sai da yayi da gaske sannan ya iya kiran Baban shima saboda kiran ya zama dole ne. "Kullu nafsin za'ikatul maut Yaya, ko da Muhammad a gaban mu yake ni da mahaifiyar sa dole sai ya mutu, bani da jahilci dan ni musulmi ne kuma na yarda da kaddara, Allah ya sa me ceton mu ne, kayi mishi dukkan abinda ya kamata a kaishi gidan gaskiya." Jiki a sanyaye Baffa ya dawo ciki, akayi duk abinda za'a yi, a daren aka kaishi. ****Sanda Baffa ya kira Baba yana daf da shiga gida, sosai mutuwar ta dake shi duka me zafin gaske, kansa a kasa kirjinsa na masa wani iri, juriya da jarumta irin ta namiji a haka suka karasa gidan, yana tunanin yadda zai sanar da Mama.    Dakin ta ya wuce kai tsaye wanda ya dade rabon shi da shiga har cikin dakin nata, tana zaune tana lissafi gabanta tray ne na abinci tana so ta kammala taci duk da tana jin kamar an dauke appetite din bakin ta ne, wani irin yanayi take jin zuciya da gangar jikin ta tamkar zatayi zazzabi, daurewa kawai take tana karfafa jikinta dan bata so ta bar aikin da take bata kammala ba. Sauri take taga ta gama dukka dan tana son kiran Tariq taji ko lafiya yake? Dan sai take jin kamar ba lafiya ba, ajiye takarda da biron hannun ta, tayi ta jawo wayarta dake saman gado ta hau dialing number sa.      Yana zaune a gajiya yake tikis bayan ya dawo daga motsa jikin sa, so yake ya watsa ruwa kafin ya duba wasu papers da zai, amma kuma ya gaza tashi yana kishingid'e kansa na dan sara masa wanda ya san stress ne na karatu da baya ko hutawa dan a sati weekends ne kawai yake samu ya huta kamar na awa hudu amma sauran ranakun sam bashi da hutu. Wayar sa dake yashe a saman dan madaidacin table dake cike da manyan text books dinsa ce tayi kara, duk da baya expecting Kira daga kowa amma sai ya mike yana dora idon sa akan table din har ya karasa ya dauki wayar ganin sunan Mama ya sakashi dagawa ya zaune a kujerar dake gaban table din yace "Hello..." "Hello Assalamu alaikum." "Wa alaikisalam." Ya amsa yana dan motsa kafarsa kafin ya gaishe ta, ta amsa sannan ta dora "Lafiya kake ko?" "Me faru mah? Lafiya ta kalou." "Naji muryar ka haka-haka, hope dai babu wata matsala." "No, stress ne kawai, da na dan samu na watsa ruwa zan warware ." "Ok!" Tace a gajarce, shigowar Baba dakin ya sakata rike maganar da zatayi, ta zuba masa ido tana karantar yanayin da ya shigo mata, zama yayi a gefen ta, sai taga kamar idanun sa sun kada "Rike wayar Tariq." Tace tana zare ta daga kunnenta, tashi yayi shima bayan ya cire wayar daga kunnen sa ya nufi wajen kayan sa, ya shiga cire kayan jikinsa. "Me ya faru?" Tace tana kallon sa "Aisha!" Sai gabanta ya ce ras jin ya ambace ta da sunan ta kai tsaye, kamar wadda aka zare wa laka haka taji, ta saddakar babu lafiya amma kuma ta gaza hasaso komai akai "Kinsan cewa rayuwa da mutuwa duk na Allah ne ko? Haka kinsan cewa bawa baya taba wuce kaddarar sa, kiyi hakuri, kiyi hakuri duk me rai mamaci ne." "Dan Allah me ya faru?" Tace hannun ta na rawa "Muhammad ne..." Sai ta mike da sauri, "Me ya same shi?" "Zauna dan Allah." Yace yana riko hannun ta, kasa zama tayi ta hau girgiza masa kai "Me ya same shi? Me ya sami d'ana." "Ya fada a rijiya, Allah yayi masa rasuwa." Kara ta kwalla da karfi, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, shikenan an kashe min d'a." Sai ta fashe da kuka me karfi, kukan da ya kai attention din Tariq kan wayar dake hannun sa yana kokarin zuba tea a cup,a kunne ya saka wayar da sauri yana sauraren abinda Maman take cewa "Sai da na nuna bana so yaran nan su je, ka dage dole sai sun je, shikenan ta kashe min shi,an raba ni da d'ana, Wayyo Aallah na." Riko ta Baba yayi, ta kwace tana matsawa baya, kamar zata zauce haka take ji, da sauri Tariq ya katse kiran sannan ya sake kira at the same time, Baba ne ya dauki wayar, ya daga "Muhammad ne Allah yayi mishi rasuwa yanzu." "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, rashin lafiya yayi?" " A'ah, tsautsayi ne ya gamu dashi,ka kwantar da hankalin ka zan kira ka." Sai ya kashe wayar, yayi saurin fita ya bi bayan Mama da ta fice da gudu tana kwala ma yaran kira. Da sauri Safiyya, Maryam da Umaima suka fito a kusan tare, Yaya dake part dinta itama ta fito a gigice, Safiyya ce ta rungume Maman da take kuka tana kiran ta kashe mata shi, kamar wadda zata zauce haka ta koma, duk suma suka saka kuka ganin Maman na kuka sosai, daka musu tsawa Baba yayi ganin sam sun maki sauraren sa, yana kokarin yayi magana amma suna kuka Maryam hadda kururuwa, shiru sukayi duk suka koma kuka kasa-kasa, yace su wuce zuwa falo, sannan ya juya, suka bi bayan sa banda Mama da ta tsaya a wajen, sai da Safiyya ta rike ta sannan suka koma ciki, duk suka zauna suna fuskar su a cikin kafafunsu suna kuka kasa kasa , Yaya ce kawai a zaune a kujera, Mama na daga kofa taki zama, Baban ma a tsaye yake ba zaka iya tantance yanayin halin da yake ciki ba, Muhammad yaro ne me matukar shiga rai, shiyasa ya shiga ransu sosai duk da karancin shekarun sa, "Dukkan mu zamu mutu babu Wanda zai zauna a duniyar nan sai dai in har lokacin mu be yi ba, amma idan yayi dole ne mu tafi, babu kuma wanda ya isa ya hana, kowanne bawa da yadda Allah ya kaddaro masa SANADIN mutuwar sa, Muhammad lokacin sa ne yayi,ko yana gaban mu ne bamu isa mu hana ba wallahi, kukan ku ba zai dawo dashi ba kuma ba zai chanja komai ba sai ma sabawa Allah da kuke kokarin yi ta hanyar kin yarda da kaddara." "Allah ya gafarta masa yasa me ceto ne." Yaya tace a sanyaye ita kanta mutuwar ta kad'a ta, dan hawaye take yi duk da bata bude murya ba, "Kiyi hakuri Aisha, kiyi masa addu'a kawai, idan Allah ya kaimu da asubah zamu tafi in sha Allah." Daga haka ya juya da sauri ya bar falon,zaman dirshen Mama tayi a wajen ta cigaba da kuka me cin rai, zuciyar ta taki amince mata ba an shirya cutar mata da yara bane dama tun farko shiyasa bata amince da tafiyar ba, waya Safiyya ta dauka ta kira gidan su Maaman, cikin kankanin lokaci sai gasu sisters da brothers din Mama har da Hajiya Babba, babu wadda ta yarda a cikin su cewa lokacin Muhammad ne yayi, dukkan su sun tafi akan shiri ne, wasu ma gani suke Aunty ce ta jefa shi a rijiyar dan sun yarda babu abinda kishiya ba zata iya aikatawa akan yayan kishiyar ta ba. A gidan duk suka kwana Hajiya Babba kawai aka mayar gida zaa dawo da ita gobe, kusan duk basu rintsa ba. Bangaren Aunty kuwa sosai jikinta ya rikice da mugun zazzabi, tun bayan da aka kaishi aka dawo ta tabbatar da gaske ya rasu ba mafarki take ba, bata san wanne kalar tunani mutane zasuyi akan ta ba amma ta tabbatar ba zata taba fita ba, me zata cewa Mama ta yarda da ita ne wai? Me kuma zata ce wa Baba da saurin yaran su yarda babu sakacin ta? "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." Ta furta da karfi sai kuma ta fashe da kuka, rike ta Innar su Saude tayi tana bata Baki "Kiyi hakuri, haka Allah ya kaddara babu makawa sai ya faru." "Me zan ce wa duniya? Me zan fadawa mutane su yarda bani da hannu a ciki? Su yarda ba sakaci na bane? Me yasa wai ma ba Usman bane ya mutun?" Da sauri ta rufe mata baki tana bata fuskar ta sosai "Karki yi sabo wallahi." "Astagfirullah." Ta hau fada da sauri da sauri, jidda da Amira dake kusa dasu suka kara tsananta kukan su, har wani jaja-jaj fuskar jidda tayi saboda kuka, fuskar su ta daga sosai, su ya bi, Usman yace su dawo shi sai ya tsaya yace zai jira su,ya akayi har ya je wajen rijiyar ya fada babu wanda ya lura shine abinda yafi damun Baffa. Gidan baki daya babu wanda ya rintsa saboda zulumi da tashin hankali, da asuba, Baba, Safwan da abokin Safwan Jamil, neighbors suke sai abokan Baba su biyu Alhaji Adamu da Malam Nura sai driver Baban suka dauki hanya, suka isa wajen 7 lokacin su Baffa sun fita har an shinfida tabarmi suna zazzaune cike da zulumin tashin hankalin da ya same su, tunda Baffa ya hango motar su Baban gabansa ya fadi, haka ya daure ya taro su, suka hadu suka zazzauna, gefen Baban Baffa ya zauna jikin sa a sanyaye, lura da yanayin Baban ya sakashi yin shiru dan da so yake yayi masa bayani amma sam Baban ya nuna babu bukatar hakan. Sun dan jima a zaune har rana ta fito sosai, sannan suke ce zasu tafi. Baffa ne ya nemi Baban ya shigo ciki su yi magana da aunty dan sosai take cikin wani hali, tashi yayi yabi bayan Baffan zuwa cikin gidan, suna zazzaune a tsakar gida da sauri Amira ta tashi tayi wajen Baban tana fashewa da kuka, rike hannun ta yayi be ce komai ba, ya isa gefen tabarmar da aka shinfida masa ya zauna sannan ya amsa gaisuwar matan dake wajen tare da Aunty duk suka tashi suka shiga ciki ya rage daga shi sai Aunty, kukan ta ne ya tsananta har ta gaza furta kalma daya ,yana jin ta be ce komai ba, har sai da ta dauki lokaci dan kanta ta rage ta shiga jan hanci. "Kin gama?" Yace yana kallon ta, girgiza masa kai tayi da sauri "Toh ya ishe ni haka, kin isa ki hana abinda ya faru ya faru ne? Ko kuma zaki iya chanja abinda Allah ya riga ya kaddara?" Girgiza kanta tayi da sauri, ya gid'a kansa sannan yace "Bana son shiririta, abinda ya riga ya faru ya faru, Allah ya jikan sa yasa ya huta, kar ku bata mana lokaci tare nake da mutane, ku fito mu wuce." Yana fadan haka ya mike, ya fice daga gidan, jikinta a sanyaye ta tashi itama, taje suka dauko kayan su, suka fito Jiddah dauke da Usman ,Amira ta rike musu kayan, Iya Lami da tayi dawowar safe na tsaye daga gefen bayan gida ta zuba musu ido,tana hasashen yadda zaa kwashe da uwar d'an idan an koma, zata so ace da ita zaa yi tafiyar dan kawai taga yadda Halima zata wulakanta dan ta tabbatar ba za'a kwashe kalou ba dan ma mijin nasu babban mutum ne me dattako. Sallama sukayi mata,ita da Innar su Saude da sauran matan, ta amsa kamar ta damu da abinda ya faru, ta rakasu har zaure tana bawa Auntyn baki, babu wanda ya kulata suka fice dan kowa ya riga ya san karya take kawai dai dan kar ace bata yi bane. Motar da Fauwaz da Jamil da Driver suka shigo ita su Auntyn suka shiga sai Jamil ya koma wajen su Baba ya zauna a gaba. Baffa na tsaye da sauran mutanen unguwar, sai matan dake mammakale a katanga, daga musu hannu su Baffa sukayi sanda aka tada motar, idanun sa akan Jiddah da itama shi take kallo, har suka bar unguwar tasu. Ajiyar zuciya Baffa ya sauke yana fatan komai yazo wa Haliman da sauki dan ya hangi tashin hankali shinfide acikin kwayar idanun ta, ya kuma san abinda take gudu da tsoro wanda har ya haifar mata da zazzafan zazzabi wanda baya raba daya biyu daga jiya zuwa yau Jinin ta yayi mugun hawa. ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (9) ***Dukkannin su suna zaune a falon, Mama na daga side din part dinta a kasa sai wata kanwar ta Anty Mimi da take ta fama da ita akan tasha ko tea ne, dan tun jiyan bata saka komai a cikin ta ba. Motar su ce tayi parking a kofar gidan da ke dauke da yan tsiraren yan uwan Baba a zaune a kasan rumfa, wajen su, su Baba suka nufa Safwan kuma da su Aunty suka shiga cikin gidan. Dukan uku uku kirjin Anty yake har suka dangana da kofar da zata sadaka da falon nasu, takalman mutanen da ta gani ne ya sakata sauya akalar ta zuwa shashen Yaya, duk nan din ma bata da yakinin abinda zata tarar, kanta a kasa hannun ta kunshe a cikin Hijab dinta ta shiga da sallamar ta wadda sai kayi da gaske zaka ji muryar ta da take a dashe sosai. Da ido Yaya ta bita bayan ta amsa sallamar har ta durkusa a gabanta, kanta a kasa tana kokarin tattaro ragowar kalaman da suka rage akan harshen ta " Karki ce komai, idan har kikayi magana akan abun da ya faru toh lallai baki san kaddara ba, ba kuma zaki ci jarrabawar ki ba, Allah ya kan jarrabi bawa ta hanyar da be yi tunani ko zato ba dan ya gwada imanin sa, ki daure ki ci wannan jarrabawar." "Nagode Yaya, nagode nagode da kika fahimce ni." "Jahili ne kadai mara tauhidi zai zarge ki, ki tsarkake zuciyar ki, karki kula kowa da maganganun mutane ki tsaya akan gaskiyarki." Shiru tayi tana jin nutsuwa na saukar mata, a kalla mutane biyu masu kusanci da Muhammad bayan mahaifiyar sa sun fuskance ta, sun kuma gamsu cewa ba zata cutar dashi ba. Sai da ta tabbatar da samun nutsuwar ta wajen kashi hamsin sannan ta bar shashen Yayan ta nufi nasu. Ta shiga duk suka bita da kallo, kallo me dauke da tarin manufofi, gaban Maman ta karasa, ta durkusa cikin yanayin da yake nuna tsantsar yanayin da take ciki, zatayi magana ta daga mata hannu dan dama tunda ta shigo bata kalle ta ba, "Bana son jin komai,cuta dai kin riga kin cutar dani, ba zan kuma taba yafe miki ba idan har cutar da Muhammad kikayi da gayya, ki fita daga harkar yayana da komai naki, bana son ko bude ido na ganki." "Allah baya barin wani dan wani yaji dadi Maman Fauwaz, kuma Allah shine shaida ta, da shi da Usman duk daya suke a wajena, ba zan taba yin abinda zai cutar dashi ba, Allah ne shaida ta, wallahi wallahi ban san ya fita ba, ina sallah a lokacin, ban kuma san baya tare da su Amira ba." "Babu abinda zaki ce fa malama, dan Allah ki tashi ki bamu waje, zaman ki anan ma matsala ce babba." Anty Nafi tace tana jan dogon tsaki "Maman Usman kije part dinki, ba komai.". Anty Mimi tace a kasan ranta tana jin babu dadi, tana kuma tausayin Haliman dan tasan ba zata taba aikata abinda yan uwanta suke zargin ta dashi, rabon ayi hakan ne ya saka har yace zai bisu, ajali ne yake kiran sa Allah ya kaddaro a chan kasar sa take. Jiki a sanyaye ta mike, ta wuce su tana jin wasu na maganganu kasa kasa, ta wuce part dinta ta shiga ta samu Jidda da Usman a zaune sunyi jigum tamkar wadanda sukayi jinyar satittika, kar ma Jidda da ramar ta sake fitowa sosai ta dashe tamkar wadda bata da jini. Karfafa kanta tayi ganin halin da yaran suke ciki, ta shiga da karfin ta tana kokarin aro jarumta ta dora a saman fuskarta wadda ta boye ainihin abinda take ciki.    Zama tayi itama a gefen Jiddan, wadda take jin su kadai suka ragewa juna a duniya, sun dan jima a haka kafin Auntyn ta mike ta nufi dakin ta, sai a lokacin wayarta da take cikin jaka ta sake daukar kara a karo na kusan hudu kenan, tun bata shigo ba aka kira Jiddan na tsoron ta fita ta kai mata taga ana ma Auntyn wani abu sai ta hakura kawai, ganin an sake kira yanzu ya sakata ciro wayar ta tashi zata kaiwa Auntyn daga cikin dakin Auntyn tace "Daga Jiddah kice bana kusa." Tsayawa tayi ta daga wayar, ta kara a kunnenta, muryarsa ta shiga chan cikin kunnenta, wani irin dum taji saboda yadda karfi da amon muryar sa ta doki kunnenta, sake maimaita Hello Aunty yayi jin ba'a yi magana ba, zare wayar tayi da sauri daga kunnen ta, sannan ta sake mayarwa a hankali cikin siririyar muryarta tace "Bata kusa." Shiru ne ya biyo bayan har ta zata ko an katse kiran ne, dubawa tayi taga yana kan layi sai ta sake maimaita wa "Bata kusa Auntyn." Samun kansa yayi da kwaikwayon muryar ta a chan kasan makoshin sa da ta tuna masa da sirantar ta, "Ina Auntyn?" Ya tambaya "Ta shiga ciki, idan ta fito zan fada ?mata." "Ok, an kaiki asibiti?" Ya tambaya yana son ji "Asibiti?" Tace sai kuma ta hau girgiza kai "A ah, ai ni lafiya ta kalou." "Ok!" Yace a gajarce sannan ya katse kiran. Dama kira yayi su yi magana da Auntyn akan abinda ya faru, yayi magana da Mama dazu, ya kuma san itama tana cikin zulumi dan kai tsaye Maman ta nuna masa Auntyn ce ma ta kashe Muhammad din, shine ya hanata yin komai, ya kuma roke ta akan kar ta tashi hankalin ta, ta kuma tashi na kowa ya nuna mata haka Allah ya tsara dama chan, dan dole ta hakura ta kuma yiwa su Aunty Nafi magana suka hakura dan da sun shirya ciwa Auntyn mutunci sosai.     Tunanin sa ne ya tsaya akan yar ficikar yarinyar, wadda be taba gani ko jin mutum me ramar ta ba, shi mamaki yake da yaji har tana magana radau haka kamar ba ita ba, a fili idan batayi magana ba zaka rantse ko kwakkwaran motsi idan tayi zata iya faduwa. Shafa sumar kansa yayi da ta soma taruwa dan ya kwana biyu be rage ta ba, ya shaki iska ya fezar yana tattare dukkan tunanin sa a waje daya, sannan ya mike daga gaban reading table dinsa ya tashi zuwa wajen system dinsa ya dauko ta ya jona a jikin socket ya kunna sannan ya shiga duba wasu publication yana kokarin dauke hankalin sa da abinda ya faru, duk da a chan kasan zuciyar sa yana tare da tausayin yaron, wanda ba zai dorar da wani abu ba game da rayuwar sa, duk rashin sakewar sa da mutane yana da matukar son yara, shiyasa yayi sabo da shi da Usman idan yana nan suna yawan zuwa dakin sa su manne masa, basu da rashin ji da hayaniya irin ta yara dai dan abinda ba zaa rasa shiyasa suke dadewa a wajen sa basu gundire shi ba, da zarar yaji zasu fara damun sa sai ya kunna musu kallo ya shige daki ya barsu wani lokacin har sai sun yi bacci sannan ya saka Safwan ko Safiyya su dauke su. Tattare aikin yayi ya ajiye dan baya jin zai iya, ya zaro socks me kauri sosai saboda sanyin da ake zugawa ya saka a kafarsa ya rufe ta da katoton takalmi ya dora rigar sanyi me kauri sosai ya fice daga gidan. **** Kasancewar karamin yaro ne ba a zauna wani zaman makoki ba Baba yace babu bukatar hakan, idan kaga Mama zaka dauka jinya tayi saboda yadda ta zabge lokaci daya haka ma Aunty, dukkan su basu da lafiya dan sai da Baba ya kira Dr Bashir yazo har gida ya duba su ya basu magani. Sati kusan biyu da faruwa abun amma babu wani sauyi a yanayin gidan, idan ka shigo gidan zaka rantse babu mutane dan ko su Amira da suke ziryar shiga part din Auntyn yanzu basa yi saboda maman, sai dai su hadu idan zasu tafi islamiyya amma ko zaman falon wajen duk sun daina, tafiya ta kama Baba satin sa guda kenan bayanan shiyasa ko zaman cin abincin ma sun daina dama shi yake assasawa shima kwana biyu kafin ya tafi ya rabu dasu dan baya son tashin hankali kuma zaman su waje daya sai iya haddasa abinda yake ta gudu. *** Tsaki Yaya taja a karo na ba adadi, lalle take kwabawa zatayi kunshi, duk gidan ya isheta so take ta yi tafiya amma tasan Baba ba zai barta ba, gashi yan hirar tata sun daina zuwa dama Jiddah ce take kawo su amma yanzu gidan kamar an yi ruwa an dauke shiru kake ji, bakin ta kaikayi yake mata kusan kwana uku kenan tana neman wanda zasu yi hira dashi amma ta rasa, Abu da take shigowa tayi mata wasu ayyukan kwana biyu taje ganin gida sai ya zama sai ita kadai. Kunshe kafarta tayi bayan ta shafa lallen a dukka kafar abinda ake kira da dungulmi ko tsohuwa ta fada kwata, ta saka leda da tsumma irin yadda tsofaffi suke, sai ga Safwan ya shigo. Sakin baki tayi tana kallon sa kafin tace "Kai nifa na zata baka duniyar nan." "Kai Yaya, ina zanje? Ina nan." "Amma ko gaisuwa? Saboda ba uwar ku bace ace babu me leko ni." "Kiyi hakuri sarauniya, kinsan yanayin da ake ciki, shiyasa amma ki basu yan kwanaki zasu ware, ni bana zama ne kwata-kwata ga kula da shop din Mama ga zuwa school?" "Menene shup?" "Shop ba shup ba Hajjaju." "Ko ma uwar menene dai." "Shago ake nufi, shine shop da turanci." "Yanzu shagon ne kuka maida shi shap saboda tsabar iyayi da kinibibi ni Hajara?" "Haka yake ai, yawanci fa kalmomin turanci ne bahaushe ya sata." "Ummm, karyar banza." "Allah Yaya, yawanci kalmomin na turanci ne." "Kaga idan kana da kati a wayar ka, kira min yayanka inaso nayi magana dashi." "Wai Ya Tariq?" "Shi, kira min shi." "Missing dinsa kike Hala?" "Musi?" Tace tana bata fuska Dariya ya kwashe da yace "Eh mana..." "Kai ka sani, idan ma zagi na kayi ruwanka,kira shi tambayar sa zan ko yana shan maganin sa, dan jiya nayi mafarkin sa wallahi." "Magani? Wait wai bashi da lafiya ne?" "Baka sani ba? Ai ba kalou kansa yake ba, shiyasa nayi yadda nayi na tabbatar ya karbi rubutu ya soma sha, kar abun yayi tsamari azo a aura masa yarinyar mutane ya bada wahala kamar yadda kakanku ya wahalar da rayuwa ta, kai gayen nan yaci ubana daidai gwargwado,me zaa yi da miskilin mutum ne wai?" Dariya sosai ta bawa Safwan, ya shiga kyakyatawa har da kusan zamowa daga kujera, tsaye tayi hannun ta nannade da leda da tsumma tana kallon shi, bata cika son dariya ba nan da nan tayi kicin kicin da fuska, da kyar ya samu dariyar ta tsaya, ya rike bakin sa ganin ta bata fuska, "Ya hakuri Hajiyata, afwan wallahi kece kika bani dariya, wato kema kinsan gaye?" "Ban sani ba, tashi kayi gaba, idan ba zaka kira min shi ba, bari ubanku yazo ai shi na isa dashi sai yakira min Shi." "Maida wukar your excellency, ni ban isa ba wallahi, bari na kirashi amma ba lallai ya daga ba, kinsan da banbancin lokaci tsakanin mu." Shiru tayi masa banza kamar ba da ita yake ba, ciro wayar sa yayi, ya shiga WhatsApp yayi dialing video call dan hakan ne kadai zai wanke shi a wajen Yayan. Jidda ce ta shigo sashen daure da food flask me dauke da alala da Auntyn tayi wa Yaya, da sauri Safwan ya mike ya karbi flask din yana mata murmushi [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (10) *** "Karka kuskura ka bude min kwano." Tayi saurin cewa ganin har ya zauna rike da flask din "Hajiya Yaya rowa dai babu kyau, gani zan me muka samu kinsan fa ni da ke akwai amana." "Yanzu na gama saka abu kaki yi, wacce amana kuma." Ta harare shi tana tabe baki, da sauri ya dauki wayar da ya manta yayi kira, yaga har Tariq din ya d'aga har ya katse kiran ma "Kinga har ya d'aga fa, na manta na kira." "Ina zaka tuna kaga kwano." Dariya Jidda tayi, ta gaida Yayan ta zauna tana kallon d'aurin da tayi a kafarta "Yaya kunshi kikayi?" "Eh yar albarka, kinsan mu bama iya barin kafarmu kod'ai kod'ai ba lalle, kiga kafa fara kal babu kyawun gani, wannan sai yaran zamanin nan, mu ina." "Yaya gashi ya daga, video call ne ma." Matsowa tayi da sauri, ta zauna a kubin sa sannan tace "Hasko min shi, kaga ba hannu." Matso da fuskar ta tayi, Tariq dake tsaye rike da water bottle jikin sa sanye da riga armless, hannun sa da yake a murde Yaya ta kalla, sai kuma ta kalli fuskar sa da take kamar kowanne lokaci tace "Menene haka kake zaune babu kaya?" "Babu kaya?" Yace a kasa sosai, amma duk da haka sai da taji, sai kuma ya kalli kanshi "Eh wannan ai sakarci ne." "Bamu gaisa ba fa Yayah, ina wuni?" Yace yana kin biye mata "Lafiya lou, kana lafiya?" "Eh, kefa?" "Oho ban sani ba." Kallon ta yayi, ta harare shi yayi saurin dauke idon sa, yana barin wajen da yake, yana jin ta tana magana da Fauwaz k'asa -kasa, yayi kamar be ji ba ya cigaba da zare igiyar takalmin dake kafarsa, "Kana ji ko? Kana shan maganin naka kuwa?" "Magani?" Sai ya tuna da sauri yace "Eh ina sha." Washe baki tayi, "Ka kyauta." Sai kuma ta rage murya ta kalli Jiddah dake zaune a dayan gefen nata tace "Maganin ya fara masa aiki.". Ya jita sarai sai yayi kamar be ji ba yace "Yayah zan fita school, zan kiraki idan na dawo." Yace bayan ya gama zare takalmin "Toh babu damuwa, ka dai cigaba da shan maganin kaji? Karka yi wasa dan aljanu mugaye ne wallahi, duk abinda kake yi nasan ba yin kanka bane aljanun gado ne." "Bye." Yace ya katse kiran,sai kuma yayi murmushi kadan, matar baki dayan ta drama queen ce, zatayi kyau da acting. Sai ya sake murmushi ya girgiza kansa yana ajiye wayar Haushi ne ya tirnike Yaya ganin bata gama bayani ba ya katse kiran, har Jiddah taso a bawa su gaisa gashi tana son ta masa wata magana amma dan wulakanci shine yace mata wani bye ya kashe "Uwar bye din, mtsw!" Tace tana mikewa "Kar ya makara school ne fa Yaya, Amma zai kira nasan yana dawowa, baki ga alamun ya chanja ba? Ai maganin yana aiki sosai." "Allah?" "Da gaske baki gani ba?" "Umm na gani fa." "Ehen, da kansa ma zai fara kiranki ne da maganin ya gama bin jikinsa." "Eh gaskiya kuma haka ne, toh shikenan yanzu ka tashi ka je, tunda yar fillon nan tazo sai muyi zaman mu.* "Abincin fa Yaya? Yunwa nake ji." Ya kai hannun sa akan flask din da sauri tace "Karka kuskura ka taba min funfulaye (foodflask) kaji na fada maka." Zare hannun sa yayi ya mike, ya daga hannun sama yace "Ban taba ba, bari naje na samo balangu me zafi da lemon exotic naci kayana nima." "Tsaya, balangu zaka siyo?" Tace tana washe baki "Eh ba, amma ko guntu ba zaki ci ba." "Haba kai kuwa, wasa fa nake maka, dauki kaci ka rage min, sai kaje ka siyo mana naman amma nawa kar su saka yaji ulcer, lemon ma bana son me gas kaji?" "An gama." Ya dawo ya dauki plate ya zuba rabin alalar ya zauna ya cinye tas, ya sha ruwa yayi gyatsa, sannan ya mike yana zura hannu a aljihu "Tunda dai ciki ya dauka, bari naje na dan yi siesta." "Wajen me naman ne sita?" "Eh eh, nan ne kuwa, bari naje." Yace yana kunshe dariyar sa "A dawo lafiya." Tace dadi na kamata, ba zata ci alalan ba har sai ya kawo balangun ta ayyana a ranta. Ido daya ya kashe wa jidda sannan ya fice yana dariyar mugunta. Shiru shiru babu shi babu alamar sa, tun da zata cire kunshin take cewa safwanu shiru, har ta gama Jidda ta zuba mata ruwa ta wanke shiru be dawo ba. "Jeki dubo min shi jidda, kar dai yaron nan wayo yayi min." "Toh." Tace tana mikewa, ta fito tana tunanin ina zata dubo shi, part din Aunty taje ta kira Usman tace ya dubo mata Ya Safwan a bangaren su, yaje ya dawo yace mata bacci yake, komawa tayi ta fada ma Yaya aikuwa ta dinga balbalin masifa da kyar ta hakura tayi shiru amma ta shirya rama abinda yayi mata. ****Washegari Baba ya dawo, kai tsaye part din Yaya ya wuce ya tadda ita tana zubawa kadangaru ruwa da abinci me manja, kasancewar part din nata ginin kurzu kurzu ne ya saka wajen ya zama matattarar gadangaru shikenan take zuba musu ruwa da abinci kullum. Shigowar Baban ya sakata dakatawa. "Sannu da aiki Yaya?" "Yawwa, dawowar Kenan?" Tace tana ajiye kwanon hannun ta, "Eh wallahi, saukar kenan Yayah, mun sameku lafiya?" "Lafiya lou ba lou ba." "Me ya faru Yaya?" "Bari na kawo maka ruwa kasha." Tace tana nufar randar ta da ta saka aka kawo mata tun daga chan wai tafi ruwan firij sanyi, kawo masa tayi ya sha yayi hamdalah sannan yace "Me ya faru Yaya?" "Uhum. Menene ma be faru ba? Gida ya zama kamar kango babu me yi da wani, fisabillillah, abinda ya riga ya faru ai ya riga ya faru ko?" "Haka ne." "Ni gaskiya bana son shirun nan, ita Halima tana jin cewa bata kyauta ba ita kuma Aishatu tana jin ba'a kyauta mata ba." "Duk nayi magana dasu wallahi Yaya, na kuma nusar da kowaccen su akan hakuri da daukar kaddara, amma ba komai zan yi maganin abun." "Yawwa, gwara duk su yi hakuri sannan su kyale yara su cigaba da rayuwar su kamar dah, shirun ya ishen baki na har doyi yake saboda zaman kadaita, na gaji." "Zaa gyara in sha Allah." "Yawwa Allah yayi albarka, shi kuma me babban suna Allah yasa me cetonmu ne." "Amin Yayah." "Bari na shiga ciki Yaya,babu wata matsala dai ko?" "Babu sai guda daya take, yaron nan ni yayi wa wayo yace zai siya min balangu, na saka rai yazo ya hanani, wallahi har mafarkin balangun nan nayi." "Kai Kai kai, be kyauta ba, yanzu yanzu zaa kawo miki balangu da tsire da kuma me?" "Leman bawo da yar ayaba." "Shikenan an gama." "Allah yayi albarka, yasa kaima yarannan su rama maka." "Amin ya Allah." ***Maimakon ya wuce part dinsa sai ya nufi bangaren su Fauwaz din ya kwankwasa masa kofa ya kira sunan sa, tashi yayi da sauri jin kiran Baba ya bude. "Mutanen garin ku, shine ka sakawa uwata rai kasan ba bata abu zakayi ba ko?" Dariya yayi shima Baban ya saka dariya "Maza kaje ka samo mata balangu da tsire, ka hado mata da lemo da ayaba masu kyau, kayi sauri kuma." Ya mika masa kudi, hannu yasa ya karba sannan yace "Ok tohm." Juyawa Baban yayi shi kuma ya koma daki ya chanja kayan jikinsa ya fito, ya dauki motar ya tafi siyo mata abinda Baban yace, tun ranar be je part dinta ba dan yasan haduwar su ba zatayi kyau ba. Part din Mama ya wuce kai tsaye, dan ba wanda ya san ya dawo, yaran duk suna falon a zaune maimakon yadda suke zama a main falon gidan tun bayan abinda ya faru Mama ta hana suna kunshe a part dinta, shigowar Baban ya sakasu duk mikewa Safiyya dake waya da saurayinta Mahfouz tayi saurin katse kiran. Bin su Baba yayi da kallo dukka yana nazarin maganar Yaya "Sannu da zuwa Baba." Suka hada baki dukka suka fada a tare, be amsa ba sai ya gid'a kansa kawai yana wucewa bedroom din Maman. Jikin su ne ya basu sai suka tashi suka shige bedroom dinsu. Umaima ce tare da Maman tana tayata jera wasu sabbin kaya da tayi a wardrobe sallamar Baban ta iske su,ajiye rigar dake hannun ta tayi, ta russuna ta gaida Baban sannan tayi saurin ficewa daga dakin. "Sannu da zuwa." Mama tace tana ajiye kayan hannun ta, ta nufo wajen Baban "Yawwa Maman Yara." Yace cikin shigar tsokana "Banji dawowar ka ba Sam." "Ai ban dade ba, na fara zuwa wajen Yaya ne, kuma dai Malam Basiru be shigo da motar ba akwai sakon da zai karbo min shiyasa." "Sannu da hanya." "Yawwa, a bani wajen zama Maman Yara." Da sauri ta jawo babban carpet din da take sallah akai me taushi ta shinfid'a masa a gaban gadon, ya zauna itama sai ta nemi gefen sa ta zauna. "Yawwa ko kefa, a bar matafiyi a tsaye?" "Ban dauka zaka zauna ba wallahi, bari na dauko ruwa da abinci." "Barshi tukunna, babu yunwa dan tun rana muka dawo na tsaya ne dai a government House, kuma Yaya ta bani ruwan randar ta me sanyi nasha." "Masha Allah, fatan an samu abinda aka je nema." "Alhamdulillah, gaskiya." "Toh Masha Allah." Sai ya gyara zaman sa "Ya karin hakurin mu?" Fuskarta ce ta sauya nan da nan, ya yi murmushi yana girgiza kansa "Alhamdulillah." Tace bayan wasu yan dakiku "Toh Alhamdulillah, Allah ya kara mana hakuri." "Amin." Tace tana jin abun na taso Mata "Abu daya nake so daga gareki dan Allah, ki cire komai ki barwa Allah, ki sani Muhammad ya tafi ba zai dawo ba, kiyi masa addu'a dan ita kadai yake bukata,maganar yaran nan da kika hana su zuwa ko ina har wajen mahaifiyarta na soke shi, ki barsu su yi rayuwar su yadda suka saba, duk wannan ba shine zai hana abinda zai faru ya faru ba sai dai idan har Allah be kaddara ba." Shiru tayi, ranta ya sosu, tasan dole Yaya ce ta fada masa, dan tasan hakan ba halin Aunty bane ko me ya faru tsakanin su bata taba fadawa Baban, tayi mata wannan shaidar sai dai kawai ba zata fada bane. "Kinji ko? Ayi hakuri a barwa Allah komai." "In sha Allah." Tace tana sauke kanta kasa, Abu daya da yake kara birge Baban da ita kenan, bata taba ketare maganar sa sai dai idan be yi ba, shiyasa yake respecting dinta sosai domin tayi masa abubuwa masu tarin yawa a rayuwar sa,da ba zai iya mantawa ba. Mikewa yayi yana karkade jikinsa, sai ta daga kai tana kallon sa "Dama dalilin zuwan ka kenan?" "A ah, zuwa nayi naga matata, uwargida sarautar mata!" Murmushi ne ya subce mata, ta tashi ta rakashi har kofar falon, sannan ta dawo ciki shi kuma ya nufi bangaren Aunty. [03/10, 21:27] Mss Xoxo: ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (12). ***Daidai gwargwado yaran sun fara dawowa kamar da duk ba dukka ba amma suna shigowa wajen jiddan ko su hadu a wajen Yaya, saura kwana uku a koma school sai ya zama kawai shirye-shiryen komawa suke tunda sabon session ne. Text books din Ss1 amira ta bawa jidda ita kuma ta karbi na Maryam a kalla an samu sauki. Duk da Baba babu laifi alhamdulillah harkoki na kara bud'e masa musamman da yanzu siyasar ta juyo kansa da gaske yake yin ta,ana kuma saka ran zai samu babban matsayi a gwamnatin tun kafin zabe yazo. Gidan da yake jikin nasu akayi masa talla bayan Maigidan ya rasu ya zama na magada, siyewa yayi ya fashe ya shigo dashi cikin gidan nasu dan so yake ya fitarwa da kowa part dinta me zaman kansa tsakanin Mama da Auntyn yadda kowa zata ci gashin kanta, sannan yana so ayi gyaran part din Yaya itama. Ana jibi zaa koma makaranta Safeera ta kira wayar aunty daga cikin wayar Mom dinta tace zato zo, kwatance aunty tayi ma Maman Safeeran bayan sun gaisa tace zata saka a kawota dan tun da akayi hutu take maganar jiddan. Ita ma jiddan tana maganar ta amma tasan ba kamar Safeeran ba dan ta damu sosai da ita, ta kan kira a wayar Aunty su yi magana. Wanka jidda ta tashi tayi, ta sake gyara dakin ta ta zauna zaman jiran bakuwar tata ko wajen Yaya bata je ba, tana zaune Usman yazo ya kirata yace tazo in ji Aunty wai kawarta tazo, da sauri ta fito ta samu Safeeran a zaune a kujera ita da wani saurayi wanda zai yi sa'an Ya Fauwaz ko ya dan girme shi, da sauri Safeeran ta tashi ta rungumeta, cikin farin ciki, dariya suka bawa su Aunty da saurayin da ya gaza boye farin cikin sa "Sannun ku da zuwa." Tace bayan sun saki juna sun zauna a tare "Yawwa." Yace idanun sa na kan jiddan, be taba ganin yarinya me kyawun ta ba, take tashiga ransa duk da shekarun ta basu kai shekarun da yake jin ya kamata ta san soyayya ba, tashi yayi bayan sun gama gaisawa yace zai je ya dawo anjima ya dauki Safeeran, har ya mike tace "Ya Isma'il dan Allah ka bari sa dare." "Ko? So kike mom ta hanani shiga gida kenan." "Ba zata ce komai ba Allah." "Da yamma dai zan dawo." Bata fuskar ta, tayi kamar zatayi kuka, ya juya ya fice yana jin dukkan wani karsashin da yake dashi yana gushewa, love and first sight kenan, zai iya jira a yadda yake ji, zuwa lokacin da ya chanchanta. Da kyar yayi driving kansa zuwa gida ya shiga falon ya tarar da Mom da wata Aunt dinsu kanwar Daddy, gaishe su yayi, ya shige dakin sa ya kwanta rigingine yana kallon sama. "I'm in love." Ya furta a hankali yana lumshe idanun sa. Gidan su Safeera babban gida ne sosai kuma suna da kudi dan Baban su babban dan boko ne kuma business man, su biyu iyayen suka haifa daga ita sai Ya Isma'il, suke nan su daga kansu Mom bata sake haihuwa. Rayuwar su suke cikin jin dadi sosai, gashi sun shaku da Ya Isma'il ko yaushe suna tare da junan su, yau ma da driver ne zai kaita gidan su jiddan amma sai yace zai kaita dan shima yaga jiddan da kullum take maganar ta, sai gashi abinda be yi tunani ba ya faru, a cikin dan kankanin lokaci ya kamu da soyayyar yar karamar yarinyar da ba dan kar yayi karya ba sai yace Safeera ma zata iya girman ta, be sani ba amma ko yanayin jikin ne dan mafi akasari fulani basu da girman jiki. Juyi ya dinga yi shi kadai ya rasa abinda yake masa dadi sam,har sai da Mom ta biyo shi jin shiru be fito ba, a tunanin ta bacci yake amma sai ta ganshi a kwance, ta tambaye shi abinda yake damun sshi, kamar ya fada mata gaskiya sai ya kasa ya girgiza kai kawai yace hutuwa yake, fita tayi sai ya tashi kawai ya bi bayan ta dan zaman haka ba zai amfane shi da komai ba. ****Zuwan Safeera yayi ma jiddah dadi sosai, ta ware sosai har ta bawa Aunty mamakin yadda ta sake da Safeera bata sake da kowa haka ba, tare suka ci abinci sannan ta ja ta wajen Hajiya Yaya, suka dade anan har Amira tazo itama tayi joining dinsu, suka saka Yaya a gaba ta dinga biye musu ana dariya. La'asar din farko farko sai ga Ya Isma'il yazo, suna part din Yayan Usman yazo kiransu, Safeera bata so ta zata zai kyaleta sai daren, dan idan sun koma gidan ma babu abinda zatayi gashi ba kowa. Turo baki tayi sanda suka shigo falon Auntyn yana zaune a kujerar dake facing hanyar shigowa, idanun sa akan hanyar yana jiran ya ga ta in da zasu bullo, ajiyar zuciya ya sauke da karfi sanda suka shigo wanda har da Aunty ta kalle shi, ya waske da sauri yana mikewa "Nace fa sai dare Ya Isma'il." "Ni kuma nace dama da yamma zanzo ai." "Muna shan hirar mu." "Wai haka jiddaaaah?" Ya ja sunan batare da ya san yayi ba "Eh." Tace tana murmushi, murmushiin shima yayi mata sannan yace "Zamu sake dawowa aunty, akwai in da zanje anjima ne shiyasa nazo yanzun." "Ba komai Isma'il, itama Jiddan zatazo in sha Allah." "Yaushe?" Ya fada da sauri, sai ya hau sosa kansa bayan yayi maganar "Ko weekends dai, tunda an koma school." "Ok, Allah ya kaimu." "Amin." "Ungo jidda, rakasu." "Tohm." Ta karbi yar madaidaciyar ledar suka fita tare, ta rakasu har wajen mota sannan ta mika ma Safeera ledar da Auntyn ta bata, ta karba tana leka ciki sannan tace ta gode. "Wai kuwa kuna da hoto tare ku biyu?" Ya tambaya bayan dogon nazarin da yayi, girgiza kai Safeera tayi ta fasa shiga motar "Yawwa Yah snap us dan Allah." "Ok." Ya ciro wayar sa, ta dafa kafardar Jiddan ya dauke su tare, yana lura da yadda kunya ta kama jiddan, yayi murmushi yace "Bari ayi ma kowacce ita kadai, na tarihi." "Yes, fara dani." "A ah bari na fara da jidda " yace yana maida wayar saitin ta,ya kashe flash din ya shiga daukar ta pretending ba dauka yake ba, sai da ya dauke ta sosai sannan ya kunna flash din yayi mata guda daya, sannan yayi ma Safeera ma. Daga nan suka tafi ita kuma ta koma cikin gidan. Suna shiga gida Safeera tayi dakin Mom shi kuma ya wuce dakin sa, ya bude wayarsa ya shiga photos ya zauna zaman kallon hotunan yana admiring kyauwun ta, idanun ta da dan karamin lips dinta shi yafi komai burge shi da ita, yana zaune yana ta kalla Farouk ya shigo, ya fizge wayar yana kallon screen din, kafin ya kalli Isma'il din irin kallon tuhumar nan, "Kana nufin... No no no it's not possible, wannan ai child abuse ne." "Inji waye? Rainon ta zanyi." "Are you serious? Wannan yar yarinyar zaka tsaya jira?" "Yes of course, menene a ciki?" "No you most be kidding, ai ba zai yiwu ba." "Kasan Allah? I'm serious, very very serious. I love her, with every bit of me,love at first sight, so mara algus kenan." "But she looks so local, beside yarinya ce karama sosai, not your type though." "Kai kaga haka, ni na san me na gani." Kifa wayar Farouk yayi a saman gadon yana zama akan couch din dake dakin ya maida kansa baya yana rufe idanunsa sannan yace "Ba zan iya cigaba da sauraran wannan tale din ba." "Yafi maka, kuma zan baka mamaki." "Allah ya bada sa'a, mu namu dai ido ne." "Yafi dai." ***Monday akayi resuming school, da wuri Isma'il ya tashi ya shirya ya fito falo ya samu Safeera tana breakfast, Mom kuma tana karasa hadawa daddy breakfast dinsa, kallon shi tayi cikin yanayin mamaki tace "Ina zaka? Kai da baka tashi sai kusan 11, ko kana da morning lectures ne?" "Safeera zan kai school." Yace yana hayewa saman dinning din, kallon sa duk sukayi da mamaki, ya share ya hau bude warmers din yana lekawa, ba zai iya cin komai ba sai ya dawo dan he's so eager ya ganta baya so su riga su zuwa har su shiga class shiyasa ma ya shirya da wuri ya samu itama Safeera ta shirya. Ajiye ragowar sandwich din hannun ta,tayi ta mike ta sakala school bag dinta a kafadar hannun ta daya tace "Na gama Mom." Mikewa yayi shima yace "Oya let's go karki makara." "Malam Sa'idun fa?Kamar yazo fa tun dazu." Mom tace cikin rashin gane kan Isma'il din. "Na hutassheshi, muje kid sis." "Ok." Tace tayi ma mom sallama suka fita tare, girgiza kai mom tayi a ranta tasan dole akwai dalilin da zai saka shi fita da safen kawai ya boye mata ne. Malam Sa'idu dake zaune a cikin mota yana jiran ta yaga sun fito ya bude motar da sauri Isma'il yace "Zan sauke ta Baba, kaje gida kawai." "Toh toh, shikenan." Ya tada motar ya fita daga gidan suma suka bi bayan sa. Suna cikin tafiya ya tambaye ta "Karfe nawa su jidda suke zuwa school?" "Umm, ina rigasu zuwa gaskiya, kaga suna da yawa sai sun gama shiryawa." "Good!" Yace yana murmushi "Na'am?" Ta kalle shi "No ba komai." Ya basar yana sake rike motar, cikin kankanin lokaci suka isa school din, kudi ya ciro a cikin wallet dinsa ya bata, "Mom ta bani fa." "Eh ku kara ke da Jidda, ku siya duk abinda kuke so." "Ok thank you." Ta karbe ba tare da ta kawo komai ba, ta shiga school din bayan ya ja motar a tunanin ta, ya tafi. Gefe ya samu yayi parking ya zauna zaman jiran zuwan su, idanun sa na kan duk me wucewa ta cikin layin, har zuwa sanda suka iso, ya bude murfin motar da sauri ya fito ya tsaya jikin motar yana kallon su, a in da yake tsaye ba zasu ganshi ba amma shi yana kallon su, Amira ce ta fara fitowa sai ita, cikin uniform din nasu navy blue da white Hijab wanda yayi matukar yi ma yar fuskarta kyau, tamkar yar tsana haka ya ganta, gashin da ke kwance a gaban goshin ta ya fito sama-sama wanda ya karawa kyakyawar fuskar ta kyau. Wani abu yaji ya tsirga masa, ya jingina sosai da motar dan ji yake tamkar yana yawo a gajimare, yana nan tsaye har suka shige cikin school din sannan ya sauke ajiyar zuciya ya fada motar ya bata wuta ya fita daga cikin line din a guje. [03/10, 21:27] Mss Xoxo: ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (11) ***Jidda da Usman ne kawai a falon tana karatun Qurani Baban ya shigo, karo na farko tun zuwan ta gidan da taga Baba a part din nasu, da sauri tace. "Baba sannu da zuwa." "Yawwa Hauwa'u, ana ta karatu?" "Eh." "Toh Masha Allah, a bada himma ko?" Daga kanta tayi,ya dauki Usman ya wuce dakin Aunty. Tana zaune jigum duk babu dadi, dawowar ta ciki kenan ta bar jidda ta usman a falon so take ta dan kwanta ko kanta dake sara mata da ciwo zai rage, sai ganin Baban tayi ya shigo dauke da usman. Mamakin ganin sa ya sakata tashi da sauri "Sannu da zuwa." Tace tana kallon shi, shima ita yake kallo, ta rame sosai tayi haske, "Kin ganki ko Halima?" Sunkuyar da kanta tayi k'asa, ya girgiza kai yana daga tsayen yace "Idan fa baki cire damuwr komai ba fa zamu bata gaskiya." "Na cire, kai na ne yake ciwo." "Ehen, kinji ko? So kike sai kin kwanta zaki ji dadi ko?" " A'ah." Ta girgiza kanta tana jin wasu hawaye masu zafi na neman zubo mata "Toh bana so, ki dawo yadda kike kiyi rayuwarki yadda Allah ya tsara miki, bakya bukatar fahimtar da kowa baki da hannu a abinda ya faru,duk wanda ma ya zarge ki kansa, ke dai ki tsarkake zuciyar ki." "In sha Allah, Nagode." "Madallah, a taimaka min na watsa ruwa na dauko gajiya, sannan a dan bani Lipton kadan." "Tohm." Tace ya juya ya bar part din, turare ta dan fesa a jikinta tabi bayan sa zuwa part din sa. ***Hannun sa dauke da ledoji niki-niki ya shiga part din Yayan, tana ganin shi ta dalla masa harara, kafin idanun ta su sauka akan hannun sa, daga mata ledar ya dinga yi ta washe bakin ta bayan ta hango ayaba, a gabanta ya ajiye ledojin sannan yace "Gimbiya Yaya ga shi inji sabon angonki, wato ni." "Me karya?" "Dan aljanna." "Kai tafi chan, d'ana ne ya siya min ba kai ba, mai alkawarin da baya cikawa tir!" "Toh ai Yaya kece da rowar tsiya, kinga ai kin bani ba dan Allah na." Jefa masa pillow din kujera tayi ya chafe yana dariya. "Bari na dauko mana plate mu bajeshi mu kwashi dadi." "Naga uban da ya isa ya taba min, wallahi baka isa ba." "Ni fa na siyo, naji kamshi amma kice ba zaki bani ba?" "Ai ba dan Allah ka siyo ba." "Ai shikenan, aci lafiya." "Ka ja min kofa idan ka fita." Tace tana tattare kayanta, ta shige uwar daki ta bar shi yana dariya. ***Da safe Tariq ya gama shiryawa cikin kananan kaya bakar long sleeve shirt da black trouser ya dora brown katotuwar rigar sanyi akai,hannun sa sanye da handsocks me kauri, sai kafarsa da ya saka socks wajen hudu ya dora brown takalmi. sake gwada kiran wayar Auntyn yayi hannun sa daya rike da cup din tea me zafi, har ta gama ringing ba'a dauka ba, a aljihun wandon sa ya saka wayar ya goya jakar da tarkacen takardun sa hade da system ke cika, ka fito ya hau lift ya sauka kasan building din, ya shiga takawa a kafa zuwa cikin makarantar da basu da nisa da gida, pcap ce akan sa da ta sauko har wajn girar sa, baya kallon kowa tafiyar sa kawai yake yana shirya abinda zai gudanar a ranar. "Hi." Ta tsaida shi ganin kamar be lura da ita ba, dagowa yayi ya kalle ta, ta sakar masa murmushi tana kallon fuskar sa "Hi." Shima ya maida mata kafin ya cigaba da tafiyar sa, da dan saurin ta, ta cimmasa, ta sake tsaida shi "Baka gane ni ba?" Ta tambaya ganin yana mata kallon wacece ke? Girgiza kansa yayi, sannan yace mata "Ban gane ba." "Okh, mun hadu a library last week har na karba pen dinka nayi signing, ka tuna?" "Oh yeah, na tuna. Sannu." "Yawwa, thank you." "Amm...sauri nake ina da meeting da supervisor dina, bye." "Bye!" Ta daga masa hannu, ya juya ya cigaba da tafiya, ta tsaya a wajen tana kallon sa har ya shige cikin building din. "Perfect!" Ta furta tana jan ajiyar zuciya. Apartment dinsu daya tun ranar da suka hadu a library ta bishi sai ta ga ashe gida daya suke shi amma yana 5th floor ita kuma tana 2nd, tun daga ranar take min duk wani moves dinsa,shi kadai yake rayuwar sa, sai abokan sa biyu daya shima dan Nigeria ne sai wani dan China, sosai yayi mata har ya zama kullum sai ta makale ta leka shi da safe idan ya fito zai tafi exercise, wani lokacin har chan take bin shi ya gama ta sake biyo bayansa su dawo tare amma bata taba bari ya gane ba. Bata da abinda zatayi a cikin school sai kawai ta koma gida ta kwanta sai da rana take da lectures dama dan kawai su hadu ya sakata fitowa a lokacin. Yau da taji muryar sa sosai sai take jin kamar an saka ta a aljanna, he has something a cikin voice dinsa da ya sakata kusan suman tsaye, very deep and sweet. ****Shigowar aunty kenan daga part din Baba ta dau wayarta, taga missed calls dinsa, ta tuna jidda ma tace ya kira shaf ta manta bata kira shi ba, yanzu kuma ya sake kira bata kusa, tasan shi da naci akan abu ta kuma tabbata magana zai mata akan wani abun tunda har ya sake kira. Kiran sa tayi tana fatan koma menene dai yasa ba babban abu bane, shigar sa kenan library yaji wayar sa da take a vibration na motsi, dubawa yayi yaga Auntyn ce, sai ya tashi ya fito daga ciki dan kar ya damu masu karatu ya sako kasan ya bi ta kofar baya zuwa wani dan karamin garden da yake cikin library din, ya zauna a cikin daya daga cikin kujerun wajen ya kira dan dama katse kiran nata yayi. Yana kira ta daga, "Tariq?" "Na'am, barka da safiya Aunty." "Barka dai, ya karatu?" "Alhamdulillah, ya karin hakuri?" "Da godiya, alhamdulillah." Ta fada a sanyaye "Na kira ranar nayi miki gaisuwa yarinyar nan ta daga." "Jiddah, eh tafada min sai na manta ban kira ba." "Mmm... Dama Aunty magana ce nake so muyi." "Toh ina jinka.* "Akan maganar abinda ya faru ne, da abinda su Mama suke cewa, kiyi hakuri pls." "Ba komai ai Tariq, ba komai wallahi." Shiru yayi kamar zai sake magana sai kuma yace "Shikenan toh, sai anjima." "Okh sai anjima." A sanyaye ta rike wayar, a kasan ranta tana godiya wa Aallah da ya saka akwai mutanen da suka fahimce ta, suka fuskanci halin da take ciki. Mutanen kuma da suke da kusanci da Muhammad idan ka dauke mahaifiyar sa. [03/10, 21:27] Mss Xoxo: ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (13) ***Wakar perfect wadda Ed Sheeran yayi wadda ake cewa I found a love, for me... ce take tashi a motar tasa a hankali wadda ta saukar masa da yanayin shauki, bi ya shiga yi a hankali tamkar dan shi da ita akayi wakar zuciyar sa fes har yaa isa gida. Yayi parking a tsanake yana cigaba da rera baitin _ "Cause we were just kids when we fell in love, not knowing what is was,I will not give you up this time.... Darling just kiss slow, your heart is all I own,and in your eyes, you're holding mine... Baby...."_ Sakin murfin motar yayi ya rufe sanda sukayi ido hudu da Daddy yana tsaye yana jin shi yana rera waka, kunya ce ta kama shi, ya hau sosa keyar sa kafin yace "Good morning Daddy. "Morning Son, daga ina haka?" "Nayi dropping Safee a school ne." "You...?" Ya nuna shi da hannu "Yaushe ka fara kai ta school ban da labari." Dariya yayi yana cigaba da sosa keyar tasa, murmushi Daddy yayi amma yasan dole akwai abinda ya sakashi chanja mind dinsa haka, "Ka kyauta sosai." "Nagode Daddy." Sai suka jera zuwa cikin gidan a tare tamkar wasu abokai. ***Tun daga ranar kullum shi yake kai Safeera school Malam Sa'idu ya dauko ta, kuma kullum sai ya labe yaga zuwan su Jiddah. Be taba bari sun ganshi ba, a hakan ya sha daukar ta a hoto dan a yanzu hotunan ta da yake dasu a wayar sa ba zasu kirgu ba, duk da yayi ma kansa alkawarin sai sun shiga ss3 sannan zai mata maganar a time din yana da yakinin zata karbe shi, hannu biyu su fara soyayyar su wadda ya tanadar mata da zazzafar soyayya. Duk sanda yake free idan a daidai lokacin short break dinsu ne sai ya siyo abubuwa ya kai ma Safeeran school yace ita da jiddah, duk da ko be fada ba ma taren zasu ci amma sai ya sake jaddadawa har Safeera ta fara suspecting dinsa, he care so much akan jiddah har ya fita ma, duk sanda suka zauna a gida sai yayi mata maganar Jidda, me tayi a school yau, me tace hirar su kenan duk sanda suka zauna ko zai koya mata assignment. Bangaren Jiddah kuwa sosai take picking karatun fiye da yadda kowa yayi tunani, duk da kusan kaso hamsin cikin dari Safeera ce dan kaf class din babu me kokarin Safeera shiyasa kawancen su ya taimakawa jidda sosai ta fanni daban -daban, hatta yanayin yadda take magana da yanayin shigar ta Safeera take kwaikwayo, shiyasa cikin kankanin lokaci ta washe a cikin class din har take iya tsayawa a tsakanin yan class din tana jin itama daidai take dasu. Abubuwa da yawa tare Mom din Safeera take siya musu na gyara da gayu,tun tana jin kunyar karba har ta dawo bata jin komai. Wani weekend tace ma aunty zata je gidan, bata hanata ba sai dai dole ta rakata har gidan ita da Usman, anan suka gaisa da Maman Safeera sannan ta bar Jiddan, suka ce zasu kawota. Murna wajen Safeera ba'a magana, da farko ganin irin gidan ya saka jikin jiddan sanyi amma kuma yanayin yadda aka karbeta ya saka ta sakin jiki dan hatta masu aikin gidan sun san labarin Jidda a bakin Safeera da Isma'il, ita kanta mom kamar zata goya ta dan murnar ganin ta, labari ya kare yau dai taga Jiddan da Safeera take bala'in so kuma kwarai ta yaba da nutsuwar ta shiyasa taji dadi da ya kasance irin kawayen da yarta take mu'amula dasu. Kamar wanda aka jeho haka Ya Isma'il ya shigo gidan,waya suke da Mom tace masa Jidda tazo ai ba shiri yayi sallama da su Farouk ya taho gida yana Allah Allah ya iso bata tafi ba. A dakin Safeera ya iske su, ya tsaya daga bakin kofa yana yin kasa da idanun sa sanda suka hada ido da Jidda a lokacin da take kyalkyala dariya, dariyar da ta saka bugun zuciyar sa tsaya chak na dan wasu dakiku. "Ya Isma'il." Safeera tace tana mikewa daga kan gadon "Look who's here." "Jidda." Ya kira sunan ta kamar wani dolo "Na'am, ina wuni?" "Lafiya lou, ashe zaki zo da gaske." "Umm.." Tace tana wasa da hannun ta, hannun ya kalla yaga yatsun ta zara-zara, juyawa yayi da sauri ya bar kofar, Safeera ta dawo ciki suka cigaba da hirar su, daga nan suka dauko books din Safeeran sukayi karatu, wajajen karfe biyar Mom tace Ismail suje su kai ta, kafin ma ta rufe baki ya mike cike da zumudi, kallon sa tayi, ya dauki car key din motar ta, ya ajiye nasa sannan yace "Bari na jira su a mota." Yayi gaba yana kada key din motar, tashi Mom tayi taje dakin ta, ta hadowa jiddah sha tara ta arziki tun daga kan underwears zuwa turare da kayan kwalliya, sai atamfa da veil, sannan ta saka mata 5k a cikin envelope ta fito ta iske su a dakin Safeeran tace su taso, turo baki Safeera tayi cikin shagwaba ya hau bubbuga kafarta kamar zatayi kuka "Dan Allah Mom ki bari sai anjima 😭." "A ah kar dare yayi, ni nayi ma Maman ta alkawarin zaa kawota, gwara ido na ganin ido ko Jidda? Kar babanku ya dawo yayi fada." "Eh." Jidda tace tana yafa dan madaidacin veil dinta "Allah ni...." Ta cigaba da buga kafarta, dariya kawai Mom tayi ta mikawa jidda kayan ta russuna har kasa ta sa hannu ta karba tayi godiya "Kuje yayanku yana mota yana jiranku, sai yaushe Jidda?" "Wataran." Tace tana murmushi "Kice ma ba zaki sake zuwa ba." Safeera ta fada tana hararar ta "Sorry mana." Tace tana kallon ta, shiru tayi dan taji haushin tafiyar da jiddan zatayi, ta bude wardrobe dinta ta dauko veil ta dora akan inner cap din dake kanta ta zura slippers suka fito hannun ta rike da ledar kayan da Mom ta bawa jiddan. Yana zaune a mota ya hango sun fito, ya cire lock din motar ya fita ya budewa Jidda baya ta side din driver, ita kuma Safeera ta shiga gaba, ta sama Mom ta hango duk abinda ya faru, ta girgiza kai kawai tayi murmushi dan dama tana suspecting Isma'il din son yarinyar yake, sai dai bata tabbatar ba sai yanzu da taga abinda ya faru, sakin curtains din tayi bayan sun fice daga gidan. A hankali sosai ya shiga driving din kamar baya tafiya ma, sanyi da wakar da ke tashi motar ta saka duk basu lura da yadda yake tukin ba, maimakon ya wuce gidan su Jiddan kai tsaye sai ya tsaya dasu sahaibco stores ya siya musu chocolates masu yawa da ice-cream sannan suka cigaba da tafiyar wahainiya har suka iso ba dan ya so ba, yayi parking suka fita tare da Safeera ta rakata har cikin gidan sannan ta dawo suka tafi gida. ***A harabar gidan sukayi kicibis da Mama, tana fitowa daga part din Yaya wanda tun sanda tazo gidan be fi sau biyu taga Maman a bangaren Yaya ba, kallon ta Maman take dan ta kwana biyu bata ganta ba, sai taga tayi shar da ita ta kara wayewa tamkar ba ita ba, durkusawa tayi a tsorace ta gaida Maman, ta amsa kamar taga kashi ta wuce ta bata sake ko kallon ta ba. Bata ji komai ba dan dama ba wai suna haduwa bane tunda ba zuwa wajen ta take ba, haka kuma ko a compound din gidan basu cika haduwa ba dan idan Mama na gida ko yaushe tana part dinta itama kuma Jiddan ba yawo take ba wajen Yaaya kawai take zuwa shima ta dayar hanyar take bi taje ta dawo. Ita har ga Allah tsoron Maman take dan ba karamin kwarjini take mata ba musamman da taga hatta Aunty ma shakkar ta take shiyasa ta shafawa kanta lafiya bata taba shiga part din ta ba ko da wasa duk nacin su Amira sun gaji sun hakura dan ita bata cika son shishigi a in da ba'a son ta ba. Rayuwar ta, ta chanja a dan lokacin nan babu abinda zata ce sai godiyar Allah dan ko a haka Allah ya barta ta gode dan bata yi tunani ko hasashen ta a irin wannan rayuwar ba, rayuwar ta ta baya ta tuna ta girgiza kanta ta furta alhamdulillah, daga haka ta wuce wajensu ta samu Aunty tana bude kayan da Mom din Safeera ta bata cike da yabawa dan ba karamin kaya tabata ba masu kyau kuma da tsada, ita kanta Auntyn tayi mamakin gidan su Safeeran dan yadda suke babu girman kai ba zaka taba zaton haka gidan su yake ba "Bafa karamin kaya matar nan ta baki ba jidda, ko wannan atamfar Babba ce wallahi." "Taki ce ai atamfar Aunty." "Tawa?" Ta waro ido tana daga "Eh cewa tayi na kawo miki." "Kai, kai hadda ni kuma?" "Eh." "Kai amma naji kunya, Nagode zan kirata dama in sha Allah nayi mata godiya, hade kayan ki kai daki." Toh tace ta tattare kayan ta kai daki sannan ta dawo suka zauna da Auntyn suka cigaba da hira. Daga nan ta kira musu Baffa suka gaisa sannan suka tashi don yin sallar magriba da aka soma kira a wasu masallatan. ***Kwanan sa hudu yana avoiding yarinyar, ta shiga rayuwar sa sosai komai yake ko ina yake sai ta bishi, gashi shi mutum ne da baya son a shiga rayuwar sa idan har ba shine ya gayyato mutum ba. Nacin ta shi yafi komai damun sa gashi sam bata da zuciya duk yadda ya kai da nuna mata baya son yadda take bin sa amma bata ganewa, shi ko sunan ta be sani ba sai ranar da ta fada masa da kanta, daga ranar be kuma sake tuna sunan nata ba ya manta. Zaman sa ya cigaba da yi a daki duk da yana da lectures amma baya son ya fita su hadu shiyasa ya hakura ya zauna yana bin lecture din online yana following komai, baya so ko kadan ya dauke idanun sa daga kan system din baki daya ya tattara hankalin sa waje daya yana yi yana jotting down key words din. Door bell dinsa ce tayi kara alamun yana da bako, ya daga kai ya kalli agogon dake makale a saman table din nasa, be san wanda zai kawo masa ziyara a irin wannan lokacin ba, duk da yasan bazai wuce Ishaq ko xuo kaiy ba, amma kuma ya san suna class a wannan lokacin kuma babu abinda zai fito dasu, sake kad'a bell din akayi, ya tashi yana jan siririn tsaki, ya shiga takawa kafarsa sanye da white socks zuwa kofar dake gaban dan corridor kafin main cikin gidan. Budewa yayi ya kalleta cike da mamakin ganin ta, basket ne a hannun ta me kyau, ta sakar masa murmushi ya dan saki fuskar sa kadan yana tsaye still akan kofar "Zan iya shigowa?" Tace tana kallon cikin gidan, da sauri ya girgiza mata kai "Ba zan iya ba?" "Eh." Yace kai tsaye, dan jim tayi a tsaye, shima ya cigaba da tsayawa a wajen sai tayi murmushi ta mika masa basket din "Lunch nayi maka naga baka fita school ba" Sai ta mika masa ya miko hannun sa ya zai karba hannun su ya hadu da na juna, da sauri ya janye yana bata fuska saura kadan basket din ya fadi abinda yayi matukar bata mamaki. "Shikenan?" Yace yana rike da basket din a kaikaice, kasa magana tayi dan tsabar takaici, ta daga masa kai alamar eh "Ok, thank you." Yace ya juya rike da basket din, ya tura kofar sa ya barta a tsaye a wajen kamar wadda aka dasa saboda tsabar mamakin sa. Kusan minti biyar ta dauka a tsaye a wajen ta gaza aiwatar da komai, kafin daga bisani cikin yanayi na bacin rai ta bar wajen fuuuu. A gaban kofar ya dire basket din, yai gaba abinda ko budewa be yi ba bare yaga abinda yake cika. [03/10, 21:28] Mamuh: _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107 [05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (15) ***Shiru yayi bayan ya ajiye wayar, mamakin sa na karuwa idan ya tuna yanayin yarinyar, tsaki yaja ya mike ya rasa dalilin da yasa shi damuwa da al'amarin ta har haka, ya kuma rasa dalilin da duk lokacin da ya ganta sai ya ji duk maganar dake dauke akan harshen sa ta dauke. Tsaki ya sake ja a karo na biyu yana dan murza saman goshin sa. Tunawa yayi da abinda yake kafin shigowar wayar, kashe datar sa yayi dan kar a sake damun sa ya cigaba da duba takardun sa har zuwa lokacin da yaji ya gaji sosai sannan ya hakura. ID card dinsa ya dauka da wayar hannun sa ya fito, ya bi ta wajen office din masu apartment dinsu da suke zama kullum Monday to Friday, jinin su ya hadu da ogan dan sosai yake son shi suna ganin shi suke fara murna shiyasa yake yawan tsayawa idan zai fita su gaisa. Ogan ne yau shi kadai a office din yana duba sabbin washing machines din da za'a kawo. Daga jikin kofar ya dan yi knocking, ya taso da sauri "Hello James." "Hello Tariq, please come in." Yace yana nuna masa ciki "No thank you, just want to check on you, i'm on my way." "Ohh, not bad." "I'll see you later." "Ok Tariq, i sent you an email, see ya." "Ok , bye." Wayar sa ya bude ya shiga mail dinsa, sai yaga wai ashe gift card ne me dauke da £80 suka bashi a matsayin lucky winner na duk yan gidan da suke bayarwa duk karshen wata, murmushi yayi kawai ya maida masa reply da "Thank you, I hope it's not cheating." Dariya James yayi dan da gaske cheating din ne, wata baturiya ce taci dan shi Tariq ko participating be yi ba amma ya bashi, reply yayi masa "It's cheating bro. Lol😅" Murmushi Tariq din ya sake yi kawai, ya maida wayar yana kara sauri akan tafiyar da yake a dah. A dan garden din cikin school din ya hangi Yasmin suna zaune da wani dan kasar ghana, so close kamar zasu shiga jikin juna, tabe baki yayi yazo zai wuce su ta tashi da sauri tana kiran sa "Tariq please ka tsaya." Dan rage tafiyar yayi har ta daidaita dashi, yaki kallon ta suka cigaba da jerawa har zuwa cikin building din, I'd card dinsa ya ciro yasa a kofar itama tasa nata suka shiga still be kalle ta ba suna dai tafiya a tare, sai da yazo in da yake son kaiwa sannan ya ja ya tsaya yana mata kallon me faru? "Please magana nake so muyi." "Ina jinki." Yayi folding hannun sa a kirji ya jingina da bangon wajen "I want us to be friends, pleaseeee." "Kin taba ganin friendship mace da namiji?" Yace yana kallon ta "Na'am?" "Yes, kin taba gani?" "Sosai, ina da friends both maza da mata, and I see nothing wrong with it." "Ok, ni I'm exceptionally different, bana friendship da other gender, it's haram in Islam, sorry." Yayi gaba abin sa ya barta a tsaye cike da takaicin wulakancin sa, juyawa tayi taga babu kowa a wajen sai su biyu, ta yi saurin barin wajen tana jin kamar ta kwala ihu, bata taba ganin dan rainin hankali irinsa ba, but ba zatayi given up ba zata cigaba da gwada sa'ar ta. ***Kanwar Yaya ce wadda ake kira da Gwaggo tazo dan taya Yayan murnar Baba ta kuma yi kwana biyu, halin su daya sak da ita da Yayan wajen surutun su, sai dai ita tafi Yaya sauki wajen fada dan Yaya akwai masifa bata ragawa kowa duk girman ka sai dai idan baka tabo ta ba. Kwanan su Mama biyar suka dawo suka bar Baba achan, a ranar kaf yan uwan Mama suka zo taya ta murna, tamkar ana shagalin biki haka aka taru Yan uwan da abokan arziki aka ci aka sha. Aunty da jidda suna bangaren Yaya anan suke nasu zaman su isu dan basu da hurmin shigarwa Maman abu. Amira ce ta kawo abinci a yar madaidaciyar kula inji Aunty Mimi tace a kawo ma Auntyn, sai kuma na Yaya shima daban. "Zo muje part dinmu, su salma sunzo duk muna dakin mu." Amira tace wa Jidda, kallon Aunty jidda tayi alamun taje? Ta daga mata kai dan ba zata iya hanata ba dan ita tun dama chan bata taba hanata zuwa ba ita dai Jiddan ce bata so,. Tashi tayi ba ason ranta ba dan dai kawai kar Amiran taji babu dadi ne shiyasa. Ta bita suka shiga part din nasu. Duk suna zazzaune a falon an baje ana ta hira suka shigo sai duk suka bi Jiddan da kallo, aunty Mimi ce tace "Amira kawarki ce tazo?" "A ah Jidda ce fa, ta gidan nan." "Ku wuce malama." Mama tace tana bata rai, "Wacece?" Suka tambayi Maman bayan su jiddan sun wuce ciki "Yarinyar chan ce ta dauko ta, yar brother dinta ce daga kauye." "Inyee samun waje tusar asuba." Aunty Nafi tace tana rike haba "Tubarkallah Masha Allah, me kyau da ita wallahi." Aunty Mimi tace tana kokarin dauke maganar Nafin "Ai ke Mimi bansan wacce irin zuciya ce dake ba, har wani kod'a kyawunta kike a gaban Yaya." "Toh laifi ne Ya Nafy? Ni fa ban ga abin tada hankali ba anan, beside har yanzu fa Ya Aisha ce a sama wajen his excellency, ko wannan kadai ya isa ai mutum ya hakura, wasu in sun yi auren ai wulakanta da gida suke, amma kiga fa ko tafiya Abujan nan Mama ce fa zata koma, tsakani da Allah mu ajiye son zuciya muyi maganar Allah, menene laifin Halima?" "Mimi bana son maganar nan dan Allah, a barta ranar farin ciki ce bana son abinda zai bata min rai." Mama tace tana mikewa "Nayi shiru." Ta rufe bakin ta, tabe baki sauran sukayi dan duk basa goyon bayan Anty Mimi kawai dan dai babu me ce mata komai kowa yana respecting dinta dan kaf gidansu babu kamar ta a kirki da son yan uwanta. ***Duk suna zazzaune wasu na danna waya wasu kuma na hira Amira ta shigo tare da jiddah, "Maryam yau ga jidda na sakata shigowar dole." "Kai Amira da kai na fa nace zan biyo ki." "Ban yarda ba wallahi." Umaima tace tana dariya "Wace ita?" Salma da tun shigowar ta taji sam yarinyar batayi mata ba, in dai taga wadda ta fita kyau a waje sai kawai taji tana jin haushin ta, tafi so duk in da taje ta zama ontop "Jidda ce, yar gidan Auntyn mu ce." "Daga kauye take kenan." Tace tana dariya "Salma." Ya Safiyya dake gefe tana chatting tace tana bata fuska "Bana son irin wannan maganar, jiddah shigo ki zauna." Ta dora tana yi wa jiddan murmushi abinda yayi matukar daure mata kai, toh ko dan dama bata cika magana bane shiyasa Jiddan ta zata ko bata da kirki ne? Jikinta a sanyaye ta zauna kusa da Maryam, sai Salma ta tashi fuuuu ta fice daga dakin. "Yarinyar nan bata da hankali, amma zan yi maganin ta." Safiyya tace tana mikewa, ta bar musu dakin ya rage daga Jidda, Amira, Umaima, Maryam sai yar gidan Aunty Mimi Nu'ayma. Sukayi zaman su har jiddah ta saki jikinta sosai dan dama Salma ce tasa ta darare da farko, tare suka ci abinci a dakin sukayi zaman su har lokacin tafiyar su Nu'ayma yayi Salma ta shigo tana kumbure-kumbure tace tazo su tafi. Biyo ta sukayi ya rage saura jidda a dakin tayi zaman ta, suna fita suka ji Aunty Nafi na fada "Akan wata bare Safiyya zata wulakanta yar uwarta yanzu Ya Aisha" "Kiyi hakuri zamuyi magana, duk wannan ba abin tada hankali bane dan Allah." Mama da bata cika son irin wannan abubuwan ba, ta fada tana kallon gefen da Safiyya take akan dinning tana duba wata magazine kamar ba da ita ake ba. Ashe biyo Salman tayi ta rar rankwashe mata kai tace kuma kar ta sake musu irin haka, shine harda kukan ta, ta fadawa uwarta shine ita kuma taji haushi take ta banbami. ***Babban Album jidda ta hango akan wata akwati, ta tashi ta dauko ta bude ta fara kalla, hotunan su ne tun suna yara zuwa girman su, sosai wasu hotunan suka bata dariya, ta dinga dariya tana kalla, har tazo kan hotunan Ya Fauwaz da Ya Tariq, tsayawa tayi tana kallon hoton idanun ta akan sa, fuskar sa kamar sanda yazo part din Antyn a duk hotunan, kamar dole akayi masa baya so. Taba kofar dakin taji anyi, ta tsaya da abinda take tana kallon kofar, turo kofar Safiyya tayi ta shigo tana kallon hannun Jiddan "Kina ciki dama jiddah?" Tace tana zama daga gefen ta, cikin rashin sakewa Jiddan tace "Ina ciki hotuna nake kalla." "Kin ganmu muna yara kanana ko?" Tace tana murmushi "Amira duk tafi bani dariya." "Ai Amira muguwar mummuna ce taana yarinya, ni da Ya Tariq ne kawai dama masu kyau." "Gaskiya." Tace tsakanin ta da Allah dan safiyyan kamar su daya da Tariq din hatta yanayin shirun su da yadda suke magana. "Bari kiga sabon Album din kwanan nan." Ta tashi ta dauko mata sabon da suka yi ranar graduation din ta, ta dora akan kafar jiddan ta bud'e mata Shine a farkon page yana sanye da dogon jeans da farar t-shirt, fuskar sa sake yayi murmushi wanda yayi matukar yi masa kyau, "Dama yana murmushi?" Ta samu kanta da tambaya "Kai sosai ma, sai dai ba kowa yake ma ba, wannan ma ni na saka shi yi wallahi." Bata ce komai ba, ta bude next page ta cigaba da kalla, kusan dukka hotunan su ne shi da Safiyya, sai wanda Safiyyan da su Amira amma nasa yafi yawa. Hotunan sun yi kyau dukka kamar zaka yi musu magana su amsa ta ciki dan yadda ya dauku sosai. Dawowa sukayi daga rakasu suka tarar da jiddan tana kallon hotunan suka zauna aka cigaba da kalla tare ana tuna baya,wanda zaa yi dariya ayi "Kinga na Ya Tariq yana karami?" Maryam tace tana dariya "A ah." Ta girgiza kai "Ya Sofy ina album din Ya Tariq dan Allah." "Salon kuyi masa dariya,ajiya ya bani ba zan baku ba." "Dan Allah jidda ce zata gani, Yaya boss yana karami." "Noo ba zan ci amana ba." "Jidda kice kinaso ki kalla zata dauko, musha dariya" " A'ah kar a dauko ni dai ba ruwana." "Kin kwafsa, da mun sha kallo wallahi." "Dan dai baya nan ne, kunsan da baku isa ba wallahi." Ya Safiyya tace tana dariya, abinda ya sake bama jiddah mamaki ganin yadda ta sake tare dasu kamar ba ita ba. Har bayan magriba tana wajensu,dan ji tayi ma kamar tayi ta zama a chan yadda taji dadin yinin ranar. Sai da Aunty ta turo tazo sannan suka rankaya tare da Amira suka koma wajen aunty, basu ga Mama a falo ba kamar ma bata nan dai. ***Kwana biyu Baba ya kara ya dawo cikin rakiyar mutane da yawa, a hanya sukayi magana da Tariq dan tun ranar be samu kansa ba, tare yake da sababbin masu kula dashi DSS har su hudu, sai wasu motocin, dole zaman sa a unguwar ba zai yiwu ba musamman yanayin aiki dole ya zama yana kusa da Mr President sannan kuma da yanayin yadda kasar ta zama dole yanzu sai an samu wadanda zasu zauna da family dinsa su kula dasu kafin ya tattara su dukka su koma chan saboda security purpose. Gidan a cike yake taf, Baffa da Iya Lami sunzo duk da be so tahowa da ita ba amma ta nace a dole sai tazo ba yadda ya iya suka taho tare har da Innar su Saude da Sauden, duk sun zo taya Aunty murnaz Baffa kuma Baba. Kafin isowar Baban gidan ya cika ba masaka tsinke hatta bangaren Yaya a cike yake da yan uwanta da na Malam, Mama ma wajen ta aciken yake da kawaye da yan uwa. Mom din su Safeera ma tazo da kanwar Daddy da Safeeraan. Aunty ce fa gayyato su duk dai dan itama bangaren ta kar ya zama babu kowa tunda su ba yawa ne dasu ba, ba kuma ta san mutanen anan din ba Duk girke-girken da akayi Mama ce ta saka akayi order ta fitar ma da Yaya na part din ta haka ma aunty sannan ta bar nata a wajenta. Ta shirya cikin shiga ta alfarma wadda tayi bala'in karbar zubi da tsarin ta, dama Mama yar gayu ce tun da bare yanzu da likafa ta daga ta zama matar minister wadda take jin a yanzu ne tayi daidai da level dinta. Itama Aunty tayi shigar ta daidai da ita tayi kyau kuma abinka da dama chan kyayyawa ce sai ta fito fes sosai. Iya Lami tana ta zak'ewa a wajen Auntyn duk da taki yarda sam da ita, Jiddah kuwa daga gaisuwa ko kallon ta bata sake yi ba, tayi zaman ta a daki ita da Safeera. Part din Yaya, Baban ya fara shiga kamar yadda ya saba ya gaggaisa da mutane. Yaya kamar ta zuba ruwa a k'asa tasha, dan farin ciki. Daga nan ya shiga wajen Mama itama da nata mutanen suka gaisa sukayi masa Allah ya sanya alkhairi, sannan ya shiga wajen Aunty a karshe. Daga nan ya dawo wajen su Baffa da aka saka rumfa a harabar gidan suna zazzaune a wajen. [11/25, 3:54 PM] Rano2: __SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (14) ***Da sauri ya karasa gaban table din,ya zauna yana jawo system din, ya cigaba da bin lectures din har zuwa sanda malamin ya gama, ya zare headphone din dake kunnen sa ya mike ya tattare komai ya ajiye a gefe ya kashe system din ya zare flash din dake makale a jiki, ya nufi wajen da kayansa suke ya dauko dambun naman da ya taho dashi ya ajiye sannan ya samo chilled juice ya hada ya zauna yana ci yana browsing a wayar sa.    Ya dade a zaune a wajen har lokacin sallah yayi, ya mike bayan ya zare socks din dake kafarsa ya nufi toilet yayi alwala ya fito ya wuce zuwa dan madaidacin masallacin da yake kusa da apartment din nasu, yana cikin dalilin da ya sakashi karbar apartment din saboda kasancewar masallacin da yake kusa da wajen, baya taba missing sallah duk da ba wai ana kiran sallar bane amma kuma yana amfani da wayar sa yaga time din idan yayi yaje yayi sallar.     Ajiye takalmin sa yayi a cikin wasu lockers sannan ya dauki wani na shiga cikin masallacin ya saka ya haura sama in da ake sallah, ka'idar su ce baa cika cikin main building din da takalmi sai dai ka ajiye shi a farkon shigowa in da aka tanadi lockers masu kyau kowa ya ajiye nasa a wajen tunda ba wai yawa ne dasu ba, Ishaq ya hango a gaban sahu ya karasa kusa dashi sukayi sallar sannan suka fito a tare, anan yake tambayar sa abinda ya hanashi zuwa lectures yau, shafa kansa yayi kafin yace "Haka nan naji bana so fita yau." "Manyan kwari dama ai haka ne, ko basu yi attending class ba lafiya lou." "Ba wani, kuma ma nayi following online, banbancin mu kawai zama a class din ne." "Eh haka Mr David yace, kayi joining class din tun daga farko." "Eh." Yace suna cigaba da tafiya. "I'm hungry wallahi, ko kana da wani abun naci?" "Muje ba za'a rasa ba ai." Yace sanda suke haura stairs din maimakon lift, ba ko yaushe yake bin lift din ba musamman idan ranar be wani yi exercise sosai ba sai ya hau stairs din kawai ko ba komai ya motsa jinin sa. "Da lift da komai amma ka bamu wahala,." "Ka motsa jini ai." "Duk wanda nake yi kullum." "Ka kara wani." Yace yana manna card dinsa a jikin kofar, ta bude suka shiga ciki, kallon basket din Ishaq yayi kafin yace "Wannan fa?" Ya nuna basket din Tabe baki yayi kafin yace "Yarinyar nan ce ta kawo." "Yasmin?" "Oh eh ita." "Wai kace nazo adaidai, har abinci take kawo maka kenan." Juyowa yayi da sauri ya harare shi "This is the first and last time, nasan ba zata sake iyayin kawowa ba." "Baka da kirki sam, yarinyar nan fa she's serious akan ka." "She's not my type." "Then wace type dinka? Kowacce kace she's not your type, sai ka fada mana type din naka muji ai." Zura mishi ido yayi, be ce komai ba kawai ya girgiza kai "Ehen ina jinka, fadi muji type dinka." "Ok, since you insist." "Ina ji?" Ya bude basket din ya shiga fito da kayan dadin da Yasmin ta aiko yana jin kamar an sashi a aljanna, ko kallo basu ishi Tariq ba, ya kishingid'a akan couch din dakin yana yin kasa sosai da idanun sa "I'm all ears." Hannun sa ya ware kamar me shirin lissafi yace "Bana son mace ta cika rama da yawa haka kuma bana son tayi kiba." "Yasmin is average.". "That's not all." "Ok ina jinka " "I want a shy girl, me kunya sosai bana son wadda idanunta suke a bude,bana son yarinyar da zata ce tana so na, nafi son yarinyar da zata zama very very hard to get, bana son cheap girl" "Ehen." "Very beautiful with a soft and long hair, me addini sosai, mara son yawan magana da hayaniya, wadda ta iya girki me dadi...." "Allahu Akbar." Ishaq yace yana tura lomar chicken biryani "Allah ya cika maka burin ka, amma fa banda hard to get din nan, dan za'a iya samun matsala." "Haka nake so ba wata matsala." "Toh Allah yabada sa'a Capt." "Amin." Yace yaja bakin sa yayi shiru dan dama ba kasafai ya fiya doguwar hira ba idan ba da Ishaq din ba.    Kallon sa ya dinga yi har ya gama cinye abincin tas ya sha ruwa yayi hamdalah sannan yazo suka shiga karatu wanda yawanci Tariq din ne yake guiding dinsa a duk abinda be gane ba, ya bala'in iya mathematics da physics shiyasa ma ya zabi bangaren aviation yana so ya gama yayi training din zama pilot in two years ya hada 1500 hours ya samu Airline transport pilot certificate. Target din shi kenan, kuma ya dauko hanyar cimma shi. Sai dare sosai ya kwanta bayan sun gama karatun Ishaq din ya tafi. ***Sabon part din da Baba ya siya aka soma ginawa wanda ginin yake sauri sosai, duk da cikin gidan aka shigo da ginin amma zai zama basu da wata alaka kowa zata zama tana bangaren ta. Mama ce zata koma sabon part din kowa ma yasan wannan, Aunty bata damu ba sam, tunda itama part din Maman za'a gyare mata a hade da main falon duk cikin nata, sai kuma a bawa su Fauwaz part din Auntyn. Sosai ginin yake sauri dan Baba so yake a gama da wuri Mama takoma a kalla ya san hakan zai rage wata matsalar. Suna zaune tare da Malam Nura da Alhaji Adamu a harabar gidan, aka kira Baba a waya, ya daga ganin number ce ta PA din Mr President wanda ya kasance class mate din sa ne, tunda ya zama shugaban kasa yake kokarin jawo Baba jikin sa amma sam Baban yaki yarda har sai da ya gamsu dari-bisa dari da yanayi da tsarin mulkin nasa sannan ya amince har aka saka sunan sa a cikin sababbin ministocin da za'a nada, babu wanda Baban ya fad'awa ya dai ce musu zai shiga siyasa su taya shi da addu'a. Daga wayar yayi suka gaisa sannan yace an aiko masa da invitation ta email sannan an yi masa booking flight zuwa Abuja a ranar shima an tura masa e-ticket din. Tashi Baban yayi bayan ya sanar dasu dalilin wayar sukayi masa fatan alkhairi sannan ya shiga gida. Wajen Yaya ya wuce kai tsaye ya sameta da maganar. Rawa ta shiga takawa cikin farin ciki, dariya Baban ya dinga yi har sai da tayi rawar ta gama sannan tace "Allah ya tabbatar da alkhairi,ya bada sa'a, ya raba ku da sharrin makiya ya baku ikon sauke nauyin da aka dora muku." "Amin Yayah, Amin ya Allah. Adduar kenan." Daga nan ya wuce cikin gida ya kira Aunty da Mama zuwa falon sa ya sanar dasu, tashi Mama tayi ta rungume shi da sauri saboda tsabar mamakin maganar, minister fa? Baban matsayi ne sosai wanda yayi daidai da ita, ya kuma dace sosai da ita. Murmushi kawai Aunty take duk kunya ta kamata, sai da Mamaan ta sake shi sannan Aunty tayi masa Allah ya sanya alkhairi. Ya amsa ya saka musu albarka gaba daya, sannan yace Mama ta hada masa kayan da zai tafi dasu kasancewar ita ke girki ranar, dakin sa ta shiga ta barsu su biyu, ya nuna mata kusa dashi yace ta dawo, ta koma ta zauna ya kalle "Har yanzu akwai abinda yake damunki ko?" Girgiza masa kai tayi, "Babu komai." "Gobe Safwan ya kaiki asibiti a sake duba ki a duba bp dinki, ban yarda da yanayin ki ba." "Allah ba komai." "Toh shikenan, in sha Allah kafin na dawo zaa yi kokarin a gama gyara gidan nan, sai kuyi min duk list din abubuwan da zaku bukata, duk da nasan yanzu zaman namu anan ba zai dade ba, amma dai bari muga abinda Allah zai yi." "Allah ya taimaka ya bada sa'a." "Amin Halimatu." Yace yana murmushi, fitowa Mama tayi fuskar ta babu yabo babu fallasa dan farin cikin da take ciki ya danne haushin Auntyn da take ji, ciki ya shiga da nufin shiryawa ya barsu a zaune suna jiran fitowar sa, babu wadda tayi magana a cikin su, har ya fito cikin shigar manyan kaya da shadda da babbar riga,ya dora dara akan sa,ya kira Safwan tun kafin ya shiga wanka yace yazo ya kaishi airport. Sallama yayi daga kofa sai da aka bashi izinin shigowa sannan ya shigo, ya russuna ya gaida Baban,sannan ya gaida su Mama. "Airport zaka kaini." Baba yace yana daga tsaye, Mama ce ta tashi ta dauko suitcase dinsa ta mikawa Safwan din, ya karba ya fita da ita, sannan shima ya sake musu sallama ya fita. Ya rage sai su biyu, Mama ce ta fara ficewa tana bata fuska, sannan Auntyn itama ta fita ta rufo masa part din,da bawa Usman key din tace ya kai wa Maman. ***Sati Baba daya a chan akayi komai ya saka hannu yayi approving aka saka ranar da za'a yi taron nad'a su wanda zai kama kwana biyu tsakani, be dawo ba sai kawai ya aika Mama da Aunty suka zo,sai Kawu Rabi'u da Alhaji Adamu da Malam Nura aminan Baban, sai Safwan. Jidda, Amira, Umaima da Maryam suka tattara suka koma part din Yaya, ta samu abokan yi aikuwa sukayi ta fama. Washegari suna zaune aka dauko maganar Tariq, Yaya ta zage tana fada musu matsalar sa ta rashin lafiya, ita a lallai sai ta yi convincing dinsu sun yarda ba kalou yake ba. Maryam ce tace "Yaya fa ras yake wallahi, kawai yanayin sa ne haka yanayin Malam dinki." "Yo wannan ai har yaci uban Malam wallahi." "Bari dai kiga a samu wata tayi wuf da kalbinsa, ba ma zaki gane shi ba." "Kayya, masu irin bakin halin nan fa basu ragawa kowa ba,matan nasu ma su suka fi shan wahala dasu." "Aiko Ya Tariq zai baki mamaki Yaya, ai shi na zamani ne ba irin Malam dinki ba." "Toh zamu gani ai, ni wallahi da ma wayata tana irin kiran nan da ake ganin mutum da sai na kirashi na sake jaddada masa maganar shan maganin nan, ku kuma duk ba waya gwara ma ni da yar karama." "Sai dai na karbo ta Ya Safiyya." Umaima tace tana mikewa "Yawwa karbo, kice tazo nan nace itama dole na tashi tsaye dan kusan bakin halin su daya da uban gayyaar." "Yanayin su ne a haka." Jidda tace ba tare da ta kawo komai ba, wani kallo Yaya tayi mata sannan tace "Eheee? Kare su kike jidda?" "A ah Yaya, kawai dai. "Kawai me?" "Ba komai." Tace tana murmushi "Yawwa, gwara ma dai karki kare shi." "Toh Yaya." Karbo wayar Safiyya Umaima tayi, ita kadai take bawa da taje ma bacci take sai kawai ta dauko ta taho. Ta kunna data ta kira shi ta mikawa Yaya wayar "Idan ya daga kiyi magana, kar kuma kice ni na kira wallahi." Karba Yaya tayi, ta mike rike da wayar tana jira ya dauka, tana kallon kanta a cikin wayar mamakin yadda al'amarin yake kasancewa na sake kamata. Ta dau lokaci tana ringing kafin a daga, fuskar sa ta bayyana a cikin wayar, dafe kansa yayi ganin fuskar Yaya ta cika screen din, kautar ta kansa yayi yana kokarin danne dariyar da ta taso masa dan duk abin mutum idan yaga fuskar Yaya a cikin wayar sai yayi dariya. "Kana jina?" Tace tana daga murya da karfi, "Ya Allah!" Ya motsa bakin sa, sai kuma yace "Ina jinki?" "Yawwa, baka iya gaisuwa bane ni wai?" "Ina wuni?" "Lafiya lou, naga ka kara haske ko mai kake shafawa ne?" " A ah Yaya, bana shafa komai." "Toh ai shikenan, baki yi min murnar Babanku ba." "Allah ya sanya alkhairi." Yace kai tsaye dan shi fa duk abinda tace kawai ahakan yake biye mata "Safiyya ce ta kira miki wayar?" "A ah Umaima ce ta aro wayar Safiya ta kira min kai tunda kai ba zaka kirani ba." "Ina Umaiman?" "Gata." Yaya ta juyar da wayar zuwa bangaren da suke zaune Da sauri ta dukar da kanta, Amira ma tayi kasa ya rage saura Maryam da Jidda kawai yake gani. Girgiza kai Maryam ta hau yi "Wallahi Ya bani na kiraka ba." Kallon su yake su biyun Yaya na sake hasko masa su a tunanin ta Umaima ce a zaune sam bata lura sun buya ba ita da Amira. Shiru yayi be ce komai ba, dan ganin figigiyar yarinyar nan ya saka shi manta abinda ma zai ce, tana nan yadda take bata sauya ba. Kashe wayar yayi kawai ba tare da yace komai ba. __SL__**       ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (16) ***Da yamma Isma'il yazo daukar su, cike da zumudin ganin jiddah, shi da Farouk suka zo yayi parking a chan gefen gidan sabo da motocin dake wajen sannan ya kira Mom a waya yana fatan su fito tare da jiddah, dan haka ma yazo da Farouk dan ya ganta a zahiri ya daina cewa ya haukace akan yar karamar yarinya. Fitowa sukayi suka tsaya a jikin motar Farouk ya kalle shi ya kwashe da dariya "Wai duk zumudin ne haka?" "Ba zaka gane ba, kwana biyu da ban ganta ba, ji nake kamar na shekara ban ga cute face din ta ba." "Uhum umm, sannu Romeo" "Ai nafi Romeo sai dai baban Romeo." "Ah lallai, sannu." "Yaww, idan ka ga babyn zaka tabbatar na iya kamu, ni zan raini kayata, ta tashi ta tsarin da nake so." "Gaskiya ne kuma, amma fa ana iya samun matsala irin haka, sai kaga karshe yarinya tace bata so." "Think positive dan Allah, in sha Allah babu abinda zai faru." "Allah yasa." Hango fitowar su Mom ya sakashi yin shiru, yana leken bayansu, ya hango su ita da Safeera a baya hannun su sarke da juna, ajiyar zuciya ya sauke da sauri Farouk ya kalli wajen da yake kalla. Har suka karaso idanun sa na kanta,shi kuma idanun Mom na kanshi tana nakaltar yanayin sa, Farouk ne ya zungure shi wanda saboda yadda yake kallon su yana murmushi har sai da Jiddan ta dan ji kunya, yayi saurin waskewa yana juyawa wajen su Mom "Mom kun fito ashe." "Ina zaka san mun fito?" Tace sai ya sosa kansa yana kallon Farouk, ya harare shi kawai ya budewa mom kofar suka shiga ita da kanwar Daddy, Safeera ta zagaya ta shiga suka sakata a tsakiya, dan russunawa jiddah tayi "Mommy ku gaida gida, sis sai gobe a school mungode." "Nifa jiddaaaa?" "Hadda kai Ya Isma'il, ina wuni?" Dadi na ya kamashi,yace "Fine, bari mu tafi." Sannan ya rufe kofar motar Farouk yayi kamar ya daki kafadar sa amma ya kyale, kamar ma Isma'il din ya manta da su waye a cikin motar. Matsawa baya jidda tayi, tana rike da hannun Usman suka juya motar ta daga musu hannu sannn ta juya zuwa cikin gidan. Shiru ne ya biyo baya, fuskar Isma'il tamkar an masa bushara da aljanna, waka ya kunna a motar ya rage volume din sosai yadda ba zai damu na baya ba, ya rike wa motar wuta yana bin wakar a hankali a hankali. "Malam ka tafi damu a hankali kar soyayya ta kwashe ka, ka zubar damu a titi." "Kyale ni." Yace yana dariya Aunty Yagana ce ta kasa hakuri, tace. "Gata yarinyar me hankali wallahi." "Wa?" Suka hada baki dukka har Isma'il din "Jidda." "Auw, eh kuwa." Mom tace kawai tana murmushi "Ai jiddah wallahi tayi, ga hankali da nutsuwa wallahi." Safeera ta dora "Bata da damuwa kwata -kwata." "Allah dai ya bar wannan kawancen naku har girman ku, har jikokin ku ma, duk da naga yayan naki ya rikice, Allah ya tabbatar mana da alkhairi Isma'il." "Na'am?" Yace yana kokarin juyowa bayan dan be yi tunanin zaayi saurin gano shi ba "Ka kula fa." Mom tace sannan ta dora "Farouk kayi ma abokin ka fada, ya rage zafafawa, ita rayuwar nan komai a hankali ake binsa." "In sha Allah Mom,ina fada masa ai." "Munafuki." Yace yana hararar sa "Wai Ya Isma'il ne...?" Sai tayi shiru tana yin murmushi "Allah yasa hakan ya kasance,." "Amin idan da alkhairi." Shiru yayi be sake cewa komai ba, yasan dole Safeera ta gayawa jiddah, shi kuma be shirya hakan ba yanzu kar tayi rejecting dinsa tun kafin ya koya mata son sa. Dole ya hanata fada mata dan sai ya jira right time, yanzu da sauran su a fara musu maganar soyayya. A gida ya ajiye su be shiga ba suka juya shi da Farouk, suna fita suka hau fada shi Farouk a lallai sai ya nuna masa is too early saboda yana jiye masa karyewar zuciya musamman a hangen sa da yanzu Jiddan suka sake yin sama, da kuma yanayin kyawunta zata iya samun yayan manyan kasar suce suna son ta (tunda shi be san jiddah ba yar gidan bace) shi kuma Isma'il yaki yarda da duk wani point da zai kawo sam, ya riga yayi nisan da ba zai gane duk abinda za'a ce masa ba. Da daddare da ya dawo gida ya samu Safeera ya kwabe ta yace kar tace ma Jiddan komai, sukayi alkawarin ba zata fada ba, akan haka suka tafi, ya kasance ita ta sani amma jiddah bata taba hasashe ko kawowa ba. Tafiyar Baba da Mama ya saka gidan ya zama tamkar part din Yaya ne kawai, anan suke duk dabdalar su tunda yanzu sun rage daga Amira sai Maryam kawai, Safiyya da Umaima sun bi su tunda su dukka sun kammala karatun su ana shirin fara higher institution, rabon zaa yi haka ne admission din Safiyya ya dinga delay karshe dole sai dai su fara tare da Umaima a wata private university din a Abujan. Da farko Mama cewa tayi ba zata bar yaranta a wajen aunty ba, sai da Baba ya bude mata wuta sosai yace toh sai ta zauna ya tafi da Auntyn dan shi ba zai katse musu karatu ba sannan ta hakura, duk da haka sai da ta kawo yar uwarta ta zauna a part dinta a zuwan ta dinga kula da su Amiran, sai gashi da ita da su Amiran duk sun maida part din Aunty da na Yaya wajen zaman su, idan akaje school aka dawo anan zaa baje har dare, daki daya yanzu Amira da Jidda suke kwana, hakan yakara karfin shakuwar su sosai. Rayuwar ta cigaba da garawa cikin ikon Allah, Jidda ta shiga Ss2 Amira ss3, anan ne Baba yace jiddan tayi waec a Ss2 din saboda yana so su taho gaba daya, jin haka ya saka Safeera tada hankalin ta, a dole itama aka kyaleta tayi a SS2 din dan ba zata iya bari jidda ta tafi, ta barta ba. Haka akayi suka zauna zaman yin waec sannan sukayi neco, bayan an gama ne jiddah ta shirya ta tafi garin su wajen Baffan ta, tayi sati uku sannan ta dawo lokacin ma Amira taje Abuja, sai ya rage sai ita kadai a gidan kamar mayya. Zaman ta da Yaya ne yake debe musu kewa dukkan su, dan idan kana tare da Yaya ba zaka taba yin hawan jini ba. Tana zaune tana kallon wata drama a wayar aunty rabin hankalin ya tattara ya koma kan kallon duk hirar da Yaya take mata bata ji ta ba, har tayi fushi ta tashi ta fito waje tana sababi "Takwara ta koya miki wannan banzan kallon kayi ta magana ayi maka banza, mtsw kuma wai a haka ake so ka koma Habuja. Ni kawai a barni na koma kauyanmu." "Ya hakuri Yaya, wallahi banji ki bane." Tace tana fitowa ta zauna a gefen Yayan "Toh naga kema da muke zama muyi hirar mu kin bi hanyar yaran chan." "Kallon da dadi Yaya." "Duk dadinsa ya kai gidan badamasi ne?" "A ah be kai ba." "Ah toh, ki daina bari na ina ta magana ni kadai" "Na daina in sha Allah." "Yawwa yar albarka, yanzu tunda an gama makaranta sai me?" "Sai ta gaba, Baba yace cigaba zamuyi." "Auw kema biya musu zakiyi ke da nake ganin ki me hankali, uban me ake tsinta ne a bokon da za'a ce sai an kure shi, shi kanshi wanchan sahoramin ina nan ina jiran dawowar shi sai na wanke shi tas, in banda shirme karatu ba na Allah da annabi ba, ace kaje kayi zaman ka ko kazo ma a kanka sai wani abu vidiyo, ta nan zaa ganka kana cika kana batsewa." "Toh Yaya yanzu rayuwar ta zama sai kayi karatun ai." "Namiji yayi mace ma sai ace dole sai tayi? Dakin mijinku be fi muku bane wai ni?" "Yaya karatun yafi." "Tafi chan, aure shine birgewar mace ba ta zauna gande-gande ba a gaban iyayen ta, yanzu ji Safiya da Umaimatu dan Allah, ga Maryama gaki ga takwara, wannan ai shirme ne." "Zamuyi ai Yaya, daga baya idan mun fara jami'ar" "Lallai ashe zaa yi fada dani kuwa, ko naji kauye wallahi na samo muku mazaje duk na hada ku dasu naga karyar bokon." Rufe bakin ta, tayi taba dariya, sannan tace "Ya hakuri Yaya, zamuyi fa." "Ko fa mashinshini baku dashi fa, wannan wanne irin abu ne? Ko wannan gattin banzan da aka zuba a waje ne yake bawa mazan tsoron zuwa su kulaku ne ni Hajara?" Sai ta hau tafa hannu tana salallami, "Ba zai yiwu ba wallahi, dole a sake sabon zama,ko za'a yi karatun dole kowacce ta kama miji a hannu, ba zan lamunci wannan sakarcin ba." "Toh Yayah." Tace tana cigaba da dariya dan ita bata ga abin ta da hankali ba, bama ta wannan tunanin ita sam wallahi, shiyasa ma bata dauki maganganun Yayan da wani muhimmanci ba. Kiran ta Usman yazo yayi yace tazo Safeera tazo,ta tashi da sauri dan bata yi tsammanin zuwan ta ba, Yaya na mata magana bata ji ba tayi gaba kawai. Da saurin ta, ta shiga falon tana kiran sunan ta, sai ta tsaya chak ganin mutum a zaune a falon jikin sa sanye da shadda fara kal, yayi kyau sai taga baki daya ya sauya mata kamar bashi ba, fuskar sa ta kalla sai taga kamar ta kara haske akan dah, "Ya Isma'il?" Tace tana karasowa dan bata ga Safeeran ba, ta bayan ta tayi tsalle ta dane ta, wanda ta kusa kaita kasa, suka kwashe da dariya gaba daya "Na zata fa ba dake akazo ba." Tace bayan ta saketa "Ni da Ya Isma'il ne, suprise visit mukayi miki tunda aka gama examz shiru." "Wallahi, duk ba dadi zaman." "Ina wuni ya Isma'il." "Lafiya lou, kina lafiya?" Yace yana dan zamowa daga jikin kujerar zuwa gaba "Ina aunty? Tasan kunzo?" "Eh ta shiga ciki, magana ce ta kawo mu Jidda ni da yayana." "Toh... Zauna bari na kawo muku ruwa." "Kyale shi, ki zauna bari naje na dauko." Tace tana zamewa ta barsu su biyu. Shafa kansa yayi jidda ta kalle shi sai tayi saurin dauke idanun ta ganin yadda yake kallon ta, ta dade da sanin yana mata irin wannan kallon amma bata taba kawo wani abu ba, amma a yau sai taga kallon nasa yayi mata nauyin da taji duk ta takura. "Jiddaaa." Ya kira sunan ta cikin jan sunan wanda ya sakata dagowa ta dan kalle shi sannan ta yi saurin dauke idonta ta amsa a chan ciki kirjin ta na bugawa kamar wadda tayi tsere, tana tsoron duk abinda zai fito daga bakin sa "Kiyi hakuri da abinda zan fada miki jiddah, ban zo ba sai da na nemi izinin Aunty, ta bani damar zuwa na fada miki abinda yake Raina.." "Jidda na jima ina sonki, so me karfin gaske, tun ranar da na dora idona akanki ban kara samun nutsuwa ba, komai nake kece Jiddah, ina sonki fiye da yadda nake son kaina, ke din nake so Jidda, ba wani abu da kike dashi ko kika mallaka ba." Wani gingirim taji a kanta, taji yayi mata nauyin da taji tamkar an dora mata gaba daya nauyin Nigeria akan ta, wani irin yanayi ta riski kanta wanda bata taba tunani ko hasashe ba, me zata ce masa? Ba zata iya cewa bata son shi ba ko dan Safeera, ko dan kaunar da suke nuna mata, sai dai bata jin ko digon sansa a ranta, bata jin zata so shi, ba kuma dan bashi da qualities din ba, ba kuma dan be hadu ba, bata taba kawo saurayi me jini a jiki da hutu kamar Isma'il zai sota ba ma, ba ajin sa bace ita, yafi ta komai da komai amma ya sauke kansa yake fada mata kalmar soyayya." "Dan Allah Jidda karki ce min a ah, zuciya ta ba zata iya dauka ba, dan Allah." Bakin ta ne ya sarke, ta shiga tari babu kakkautawa, duk ya rikice ya shiga kiran Safeera, da sauri ta fito ganin jidda na tari ta koma ta kawo ruwa ta bata tasha sannan tarin ya tsaya. Kallon ta yake yana daga tsaye yaki zama saboda yadda ya rikice,sai da ya tabbatar ta dawo daidai sannan ya zauna yana jan ajiyar zuciya. [03/10, 21:27] Mss Xoxo: ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [05/10, 16:20] Billyn Abdul 2: *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ ** *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (17) ***Shiru ne ya biyo bayan zaman, kowa da abinda yake sak'awa a ransa. Safeera ce ta gaji da shirun ta mike "Ya Isma'il muje sai muyi waya ko Jidda?" Gid'a mata kai jidda tayi, tana kallon Safeera taje tayi wa Aunty sallama tazo suka fice ita dashi tana zaune kamar wadda aka dasa a wajen. Aunty ce ta fito ta sameta a zaune a wajen kamar wadda aka ce karta motsa daga wajen, kunyar Auntyn ce ta lullube ta, ga wani irin yanayi da take ciki me wahalar fassarawa "Jidda ba dai korar su kikayi ba ko?" Girgiza kanta tayi sannan tace "A ah Aunty." "Toh ya akayi? Bani labari." Dariya ta bawa Jiddan yadda ta zauna tana kallon ta, tana jiran ta bata labari "Ni suka fara samu da maganar jiddah, da farko ma mamaki nayi a tunani na Ismail yafi karfin ki, ban taba kawo hakan ko a hasashe na ba, kina ganin zan bari wannan babbar damar ta wuce mu?" "A ah." Tace a sanyaye "Shiyasa na bashi dama kuyi magana duk da nasan halin ki, ba lallai ma ki bashi wannan damar ba." "Uhum." "Muyi addu'a mu nemi zaɓin Allah, idan da alkhairi Allah ya tabbatar mana." A ciki ta amsa, ta tashi ta shiga ciki dan tana bukatar zama ita kadai tayi tunani sosai. ***Tun bayan tafiyar su aunty take jujjuya maganar a ranta ta rasa Wanda zata fadawa, a yau take saka ran zuwa Baban, weekends yake zuwa Kano sai yayi kwana biyar a Abuja, ta gama duk abinda zatayi tunda tasan ko yazo ma sai ya gama da mutanen sa a waje sannan yake shigowa ciki, jidda tayi kulewar ta a daki yan miskilancin sun motsa sai ta kyale ta tayi nazarin abun sosai.    Yanke shawarar zuwa wajen Yaya tayi kawai ta rage zaman kadaitar, ta yafa mayafin ta ta nufi shashen Yayan, ta sameta a zaune ita da aabu suna zare ganyen zogale daga jikin sa, sa hannu tayi aka cigaba tare da ita suna hira har aka gama tas abu ta dauka ta tafi kicin ta dafa mata. Fitar abun ya saka Auntyn yin shiru tana tunanin sanarwa Yayan abinda yake faruwa da yake ya nukurkusar zuciyar ta, yanke shawarar sanar da Yayan tayi kawai dan idan abu na cin ka idan baka fada ba baka taba jin dadi. "Yaya kin gane kawar Jidda Safeera ko?" "Na gane ta, bikin ta yazo ne?" "A ah, su ai yan boko ne Yaya." "Ai sai ayi tayi dai, yaran nan jiran Alhaji nake yazo ayi wacce za'a yi, ko zasuyi karatu sai sun fara fidda miji, dazu muna maganar da jiddah dariya ma ta mayar da abun." "Gaskiya ne yaya." "Toh Allah,zaka bar zagada-zagadan yan mata ne a gabanka haka? Wannan ai shirme ne." "Ita Jidda dama maganar da zan miki kenan, Yayan kawarta ta, Ismail yazo yace yana son ta." Da sauri Yayan ta kalle ta kamar bata shirya jin hakan ba, kamar kuma ba ita ke maganar a samu miji yanzu ba "Ita Jiddan ce tace yazo?" " A'ah, shine dai ya sameni da maganar, shine nace bari na fara fada miki." "Toh ita Jiddan tana son shi ne?" "Wallahi Yaya ban sani ba, amma dai kinga yadda suka shaku da kanwar sa, kuma suna son Jiddah sosai har mahaifiyar su wallahi, shiyasa nayi mata sha'awar shi." Shiru Yaya tayi, ta bata fuska nan da nan tayi kicin kicin, hakan ya bawa Aunty mamaki ta rasa dalilin hakan daga Yayan, kasa hakuri tayi tace "Baki ce komai ba Yaya." "Toh me zance? In dai tana so kuma an tabbatar da halin sa ai shikenan." Shiru duk sukayi, ganin kamar ran Yayan ya baci sosai ya saka Auntyn tashi ta tafi, tana fita Yayan ta mike itam "Ai ba zata sabu ba wallahi, gida be koshi ba a kai dawa, yarinya me hankalin zan bari ta kubce mana ina, bari ubansu yazo." A fili take maganar tana tsaye, sai ga Fauwaz kamar wanda aka jeho hannun sa rike da ledar wayar Jidda da Baba ya siya musu ita da amira na gama school, sai kuma sakon snacks da Mama ta bayar a kawo ma Yayan. Tafiya yayi da dan sassarfa kamar zai rungume Yayan ta goge tana dariya "Shakiyin banza, shakiyin wofi, rungume ni fa zakayi da ko?" "Eh wai irin na turawa ba, irin nayi missing din nan naki." "Allah ya shirye ka kaji, zuwan Kenan?" "Wallahi Yaya, zuwan kenan dan Baba ma ya tsaya wani meeting ga wata gaisuwa da zasu kawai nayi gaba dan na matsu naga my heart beat." Ya tallafe zuciyar sa, bugu ta kai masa ya zille yana kyalkyala dariya "Zo ka zauna dama neman wanda zan fadawa damuwa ta nake sai gaka." "Faduwa tazo daidai da zama, ga sakon ki inji Hajiya Mama, part din ki kuma ya kusa kammaluwa na daina missing dinki." "Toh ajiye nan tukunna, an gode." Ajiyewa yayi ya zauna, itama ta zauna tana tattaro hankalin ta waje daya kana gani kasan magana zatayi me muhimmanci "Ya labarin Yayan ku?" "Lafiya kalou, ya gama ai har ya fara training, kinsan wasu awowi ake so ka hada kafin ka zama babban matukin jirgi." "Shi kuma abin da ya dame shi kenan, saboda tsabar rashin son mutane shine ya zabi bangaren da ba zai dinga zama ba kenan koyaushe yana sama kamar tsuntsu." "Da dadi fa Yaya, babban aiki ne." "Kai ka sani, ni ba wannan ba, zaka iya kira min shi yanzu?" "Yanzu nasan baya kusa dan dazu muna magana ma ya kashe zai kirani." "Toh shikenan, wai kuwa yana da budurwa ni Hajara?" "Tab! Ba dai Ya Tariq ba, karatun ya saka a gaba idan fa ba gani yayi ya karbi cert dinsa a hannu ba, toh fa ba zai nutsu ba, yana da naci duk abinda yasa a gaba." "Toh Masha Allah, wani tunani nayi. Zan je takanas na roka masa auren Jidda a wajen mahaifin ta." "Jidda kuma Yaya?" "Ita, dan Malamin da ya bashi rubutu ya fada min, idan aka basshi haka sakaka toh ko auren ma ba zai ba, haka zai kare rayuwar sa, ni kuma sai na duba kaf dangi babu me halin Jidda, ita kadai zata iya taimaka mana ta rufa mana asiri." "Amma Yaya Jiddah fa, da Ya Tariq?" "Menene a ciki?" "Ba komai, amma a fara jin ta bakin ta kar ayi mata dole." "In sha Allahu ma babu wata matsala, ina ji a raina zasuyi rayuwar aure ingantacciya." "Toh yanzu ta yaya hakan zata kasance?" "Ni dai kai zaka taimaka min, ka sami Jiddah da maganar naga kuna shiri sosai, ni kuma zan fadawa Baban KU." "Toh Ya Tariq din fa?" "Karka fada masa, irin matsalar sa ai baa fada musu sai dai kawai ayi dan aka daka ta tasu wallahi ba za'a yi ba." "Auren dole kenan za'a masa." "Dallah ana kaika." "Toh ai Yaya abin ne, nasan halin ya Tariq da taurin kai, kar ya bata ma yarinya lokaci azo ba'a barta ta zabi miji da kanta ba shi kuma yazo yace ya fasa." "Ai wallahi ina me tabbatar maka be isa ba, kai dai kawai kayi abinda nace, sauran ka bar komai a hannu na, Dijengala nake me abun mamaki " "Toh Allah ya taimaka dije." "Ka fadi sunan uwarka." "Hahaha, Allah sai na fasa taimaka miki." "Yi hakuri toh." "Ban hakura ba, sai kince please." "Ni zaka wulakanta dan zaka taimaka min?" "A ah, amma sai kin bani hakuri da turanci." "Kasan dai bana son shegen turancin nan? Kaga ana ciccize baki wai a dole ana turanci, mtswws! Aikin bur inji tusa." "Shikenan tunda bakya son taimako na, kuma sai na fadawa Ya Tariq abinda kike shirya masa idan yaso ya hawo jirgi yazo ya sameki." "Yazo din mana, tsoron sa nake? Karka taimaka din idan baka taimaka ba ai ubanka zai taimaka tunda shi na isa dashi." "Calm down My heart beat, wasa fa nake miki, ai ban isa naki abinda kike so ba, yanzu zanje na fara aikin ki." "Yawwa dan albarka, yi maza ka gama kai ma na samo maka taka ko a karkara ne." "Wait what? Wallahi kar ma a fara dan ina da fine babe dita idan ba haka ba kuwa zan bar gari na hada kayana na tafi karkashin gada." "Ka tafi bangon duniya ma, dan nema." "Maimakon ki lallaba ni,o matar nan." "Ba zan lallaba din ba, nima ba uban da ya lallaba ni da za'a auran min dunkum din kakanku." Da sauri ya sa hannu ya toshe bakin sa saboda yadda ta bashi dariya sosai, ya mike ya fice dan idan ya biye mata ba zata gaji ba sam. Tsohon part dinsu ya shiga, ya ciro sabuwar wayar Jidda ya bude ta, ya tura hotunan Ya Tariq masu yawan gaske sai nasu dasu Amira dan kar ta kawo komai, sannan ya kashe ta, ya maida ita kwalinta, ya nufi bangaren Auntyn. Jidda na kwance a daki tayi rigingine taji usman na ihun ya Fauwaz, da sauri ta duro ta fito ta same shi a tsaye ya daga Usman sama yana dariya. "Ya Fauwaz." Tace ya sauke Usman yana mata murmushi "Jidda ce tayi kiba haka?" Yace a sigar tsokana, dariya ta saka "Kai Ya Fauwaz yaushe ka ganni last zaka ce nayi kiba." "Allah kuwa, idan na ganki a hanya ma ai ba zan gane ki ba." Dariya kawai take dan tasan hadda tsokana, duk da tasan tayi mugun chanjawa sosai dan baki daya jikinta ya murje duk ramukan nan sun ciko sai wanda ba za'a rasa ba. Bangaren chest da bayanta a lokaci daya tayi su dan bata taba ma tunanin zata yi ba, girman lokaci daya yazo mata shiyasa yanzu koyaushe da Hijab dinta take yawo a cikin gidan saboda ma'aikatan da masu gadin gidan. Ledar wayar ya mika mata ta karba tana leka ciki, tayi tsalle cike da murna, "Sakon Baba,." "Mungode Allah ya kara budi." "Amin Amin, Amira ma jiya aka bata tata, number ta na ciki tace ki kirata kina kunna wayar akwai gist." "Toh shikenan, yau ba zan iya bacci ba, kusan kwana zamuyi muna hira nasan." "Lallai gandoki, zaku yi ku bari ne, ina Aunty ta shiga?" Ya waiga yana kallon bangaren bedroom din Auntyn "Tana part din Baba." "Ok, gidan shiru,kuma ku tattara ku dawo ma dinga zuwa hutu kawai." "Aikuwa." "Shine, dama akwai plan din Baba, amma wannan zuwan nasan har da magaanar tafiyar ma, kinga ya maida hankalin sa waje daya ya dinga zuwa ko duk after two weeks ne, yanzu kuwa yana chan hankalin sa na nan." "Ai kamar Yaya ce bata son tafiya ko?" "Haka zata hakura, an gama.mata part dinta ma fa." "Lallai dole ta hakura." "Aikam, in baki labari." Yayi kasa da murya "Nayi new babe wallahi." "Dan Allah, aina take?" "A chan Abujan ne." "Lallai, Masha Allah." "Ki bari kawai, zuwa zan na shige daga ciki, na bar Ya Tariq tunda shi ya tsaya kure wa boko guda." "Be gama ba har yanzu? Ya dade." "Ya gama wani course yake, kinsan pilot ne." "Wai, ban ma sani ba ai." "Aiko yana chan ya kusa ma, dazu muka gama waya ma." "Allah sarki, idan kunyi waya ka gaishe shi." "Gaki da sabuwar wayar ki, na ma saka miki number kowa har tasa, ki kirashi kawai." Zaro ido tayi "Wai... Tsoron sa nake ji, ba zan iya ba wallahi." "A ah zaki iya mana, menene abun tsoro?" "Uh um, ka gaishe shi kawai." "Toh shikenan, zaiji." "Nagode." "Bari na dubo Jamil mu gaisa, zan dawo idan aunty ta fito." "Ok sai ka dawo." [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (18) ***Tunda suka shigo mota be kara magana ba, tsoron sa daya kar Jiddah taki shi, be san ya zai yi da rayuwar sa ba idan har tace bata son shi. Da kyar ya kaisu gida suna zuwa yayi saurin yin hanyar dakin sa, jiki a sanyaye itama Safeeran tayi nata dakin tana fatan kar a samu matsala dan ta san yadda Ya Isma'il yake son Jidda. Tunda ya shiga dakin ya kasa zaune ya kasa tsaye,duk da ba wai tace bata son shi bane, amma kuma ai be kamata ta rikice haka ba, ya kamata ko yaya ne ta bashi amsa. Wayar sa ya dauka ya kira Farouk yace ya shigo dan Allah, nan da nan sai gashi, ya kwashe komai ya fada masa , shiru yayi yana nazari kafin yace "Kila shock ne, kasan har yanzu fa da sauran su, kila bata taba tunanin hakan ba shiyasa tayi acting haka, give her some time, in sha Allah Khair." "Kana ganin ba matsala, tari ne fa ya sarketa kamar zata shid'e." "Calm down, ina ji a raina ba matsala bace gaskiya, ka bata time ka barta da Safeera suyi magana, kawarta ce tafi kowa sanin ta, hopely zata iya convincing dinta ma." "I hope so, I'm just nervous ne, ba zaka gane ba. I don't think zan iya daukan rejection." "Ba matsala fa, ka kwantar da hankali ka, as you come fine like this akwai wata babe da zata ki ka ne?" "A ah fa, banda irin Jidda." "Hadda wadda tafi Jidda ma." "Kana dai fasa min kai ne kawai." "Da gaske fa " "Toh naji, bari na duba me akayi a kitchen yunwa nake ji yau ko breakfast ban ba." "Kaji ko?" "Bari kawai." Yace ya fita shi kuma ya mike kafarsa yana tausayin Isma'il din idan har aka samu matsala. ***Zaman jiran Baba yayi tayi har bayan isha, sannan ya shigo a gajiye duk da haka sai da ya tsaya a wajen Yayan dan yasan tana nan tana jiran sa, a zaune kuwa ya sameta tana kallo tana dan gyang'adi, sallamar sa ta sakata wartsakewa ta mike da sauri "Yaya baki bacci ba, Allah yasa bani na rike ki ba nasan da wuri kike kwanciya." "Kai nake ta jira wallahi, sannu da hanya." "Yawwa, ai da kin kwanta idan Allah ya kaimu da safe sai muyi maganar." "Ba zan iya hakura bane ai, magana ce me muhimmanci." "Toh, Allah yasa lafiya " Yace yana zama a kasan carpet din,daga gefen kafarta, baya taba zama kujera da mahaifiyar sa tunda ya taso, yana bala'in so da kaunar Yaya dan baya hada duk wani abu da ya shafe ta da kowa har kuwa da yayan cikin sa, shiyasa duk abinda take so shi yake mata. Gaba daya ya tattaro hankalin sa waje daya ya kara tankwashe kafarsa, dan yasan idan ba fada masa matsalar Yaya tayi ba ko baccin kirki ba zata iya ba. "Maganar yaran nan ce Alhaji." "Ina jinki Yaya." "Ajiye 'yaya mata a gaba haka be kamata ba, ba daya ba har su biyar rigis, wanda duk cikin su babu wadda akayi wa aure ba zata zauna ba, abun nan kullum dashi nake kwana nake tashi, ya zama lallai duk su fito da miji ko da za'a yi karatun dai ya zama akwai maganar aure." "Haka ne Yaya, dama dai akwai maganar Safiyya da Umaima a k'asa." "Ah toh Masha Allah, ai ban sani ba, sai ayi abinda ya kamata, daga su sai azo maganar na k'asan." "Wai da suma su fara jami'ar, tunda Maryam ta fara yanzu tana ajin farko, Amira da Hauwa'u kuma zasu fara suma bana,sai a hade su, su uku idan sun kai ajiye biyu ." "Hakan ma yayi, amma ni ina da wata alfarma da nake nema a wajenka, buri na kenan idan ka cika min burin nan ka gama min komai." "Babu alfarma a tsakanin mu Yaya, me kike so ayi? Fada kawai zakiyi ni kuma zan cika miki da yardar Allah." "Magaanar yaron nan ce Tariq, da yarinyar nan Jiddah." "Na'am!" "Na duba na dubo gaba daya dangi kaf banga wadda ta dace dashi ba, sannan na gamsu da tarbiyyar yarinyar nan dari bisa dari, ina kaunar ta har cikin raina bana so mu rasa ta, shine nake so ka kaini wajen mahaifinta na nema wa Tariq auren ta." "Toh Yaya, duk yadda kika ce haka za'a yi, da ni da yaran nan duk ikon ki ne." Washe baki tayi cikin tsananin jin dadi tace "Allah yayi maka albarka,ya raba ka da duniya lafiya, ya sa yaran nan su rama maka." "Amin Yaya." "Yanzu yaushe zamu je?" "Toh Yaya, ko wani satin idan Allah ya kaimu, sai muje." "Toh shikenan, Allah ya kaimu." "Amin ya Allah, Allah ya tabbatar mana da alkhairi." "Amin Amin,sai da safe." "Allah ya tashe mu lafiya." ***A daki ya samu Aunty, ta tare shi da fara'arta, ya fara watsa ruwa ya zura sabuwar jallabiyar sa sannn ya dawo falon ya zauna, abinci ta kawo masa wajen da yake zaune, yaci kad'an dan cikin sa a chushe yake, ta tattare ta kwashe ta maida kitchen sannan ta dawo ta zauna a gefen sa, zuciyar ta na azalzalarta da maganar Jiddah, kallon ta yayi yaga kamar akwai abinda zata fada masa, sai ya ajiye remote din hannun sa ya tattara hankalin sa ya bata yana fuskantar "Ya akayi Halimatu, kamar da magana a bakin ki." Murmushi tayi ta sauke kanta k'asa, "Yanzu na baro wajen Yaya, tazo min da wata magana me girman gaske, duk da na amsa mata da toh dan dole a lallaba ta, amma kuma ina hasaso gaba, duk da ni kaina na dade ina hasaso dama hakan ta kasance a raina, amma na share saboda sanin halin yaran yanzu ba irin mu bane, kar kayi musu abu su ga kamar ka takura musu, shiyasa nayi hakuri na bar magaanr a raina, amma kuma sai ga Yaya tazo da maganar, kuma ga dukkan alamu idan har aka ki yi mata abinda take so za'a samu matsala." "Toh, Allah yasa ba wani babban abu bane." "Babba ne a wajen yaran idan har aka samu akasi, amma kuma idan suka hada kansu zan fi kowa farin ciki da wannan hadin." Kanta ne ya kulle bata gane in da Baban ya dosa ba, ganin bata fahimta ba ya saka shi yi mata gwari-gwari. "Yaya ce take so muje mu samu Yaya, a nemawa Tariq auren Jidda." Wani gingirim taji kanta yayi, ta kalli Baban sannan tace "Tariq kuma?" "Eh." Ranta ne ya dan sosu, har Baban ya fuskanci bata ji dadin maganar ba, duk da bata ce komai ba amma fuskar ta, ta nuna rashin jin dadinsa. Ido ya zuba mata cike da mamakin yadda ta karbi maganar, a tunanin sa zata fi kowa murna da hakan dan ko ba komai Tariq dan dakin tane, sannan be yi tunanin zata ki jinin sa ba, tunda duk tsiya ai Tariq dan sa ne, kuma idan da kara itama ai dan ta ne "Akwai matsala ne?" Yace mata fuskar shi na sauyawa zuwa bacin rai, girgiza masa kai tayi kawai. Sai ta mike ganin ba zata iya rike abinda take ji ba, ta fice daga dakin ya rakata da ido cikin tsananin mamaki. Daki taje ta zauna ta rasa abinda yake mata dadi, bata taba kin Tariq ba, ba kuma zata taba kin sa ba, amma Mama fa? Ya rayuwar Jidda zata zama a auren wadda mahaifiyar sa bata so ko kaunar ta? Har ga Allah tafi wa Jidda sha'awar Isma'il, tunda shi da mahaifiyar sa duk suna san jidda, zata fi samun nutsuwa dasu dan zasu tallafi rayuwar ta, sannan zata samu uwa da zata dubi lamuran ta. Safa da marwa ta dinga yi a tsakanin dakin ta, shiyasa Yaya dazu ta bata rai kenan akan maganar, shine tayi saurin fadawa Baban, da tasan hakan ne zai faru da bata yi mistake din fara sanarwa Yayan ba, dama ance ciki ba dan abinci kawai aka yi shi ba, da ta sani ta rike sirrin su ya zama tsakanin ta ne kawai da Jiddan har zuwa sanda zasu fahimci juna daga nan duk abinda za'a yi sai ayi. Yanzu ya zatayi? Zata cewa Baba a ah ne bayan abinda yayi wa Jiddan da bashi da maraba da abinda yayi wa Yayan cikin sa, ko zasu ki dansa Tariq ne bayan shi be kyamace su ba. Ko kuwa Baffan Jidda zai hana dan Baba auren Jidda ne? Bata da mafita, mafita daya ce idan har jidda taki, amma kuma tayaya ma Jidda zata ki? Baba ko Yaya su nemi alfarma a wajen ta, ta kasa yi musu. Ai da ta cika babbar butulu kuwa. Har kusan awa daya bata koma dakin Baban ba,tana ta sakawa da kwancewa har bata san lokaci yaja haka ba, dakin Jiddan ta shiga a tunanin ta ko tayi bacci dan tana da baccin wuri, ga mamakin ta, idanun ta biyu tana kallon hotuna a wayar ta, akan hoton Tariq take, jin Auntyn ya sakata saurin kifa wayar amma duk da haka Auntyn ta riga taga abinda take yi, maimakon tayi abinda ya kawo ta dakin sai kawai ta fice ta jawo mata kofar. Tashi Jidda tayi dan tunda ta zauna take kallon hotunan Ya Tariq dake cikin wayar, har sai da Auntyn ta shigo sannan ta dawo senses dinta, takashe wayar ta makala ta a charge ta kwanta ta rufe idanun ta, maimakon tayi bacci sai ta samu kanta da tunanin sa, ta dinga juyi tana so baccin ya dauke ta amma sam, haka tayi ta fama har dare ya tsala sosai, da kyar bacci ya dauke ta. Tashi tayi da safe idanun ta a kumbure saboda rashin bacci, ta gyara dakin ta dan yanzu part din Auntyn baki daya masu aike ne ke gyarawa. bayan ta gama ta fito falo ta zauna kenan tana kallon TV Ya Safwan ya shigo, ta gaishe shi ya amsa yana nuna mata fuskar ta "Me ya faru da face dinki?" "Bacci ne wallahi." "Wai da gaske kike dama da kika ce raba dare zakuyi da Amira kenan." "A ah, wajen 9 fa muka gama waya da ita, sai kuma baccin yaki zuwa." "Kina me? Kallo ko?" "A'ah, hotunan daka saka min na zauna ina ta faman kalla ashe har dare yayi ban sani ba." "Ah shiyasa, kinga ai kin more kallo." "Kai Ya Fauwaz." "Allah kuwa." "Fauwaz." Aunty ta kira sunan sa tana shigowa, kallon kofar yayi dan jiya be dawo ba, da yaga dare yayi sai kawai yace ya shigo da safe. "Ina kwana aunty?" "Lafiya lou, ashe tare kuke jiya da Baba." "Eh wallahi, wajen Jamil naje kuma sai muka tafi wata sabgar sai dare muka dawo." "Lallai, an kwana biyu ai ba'a hadu ba." "Wallahi." "Ya kowa da kowa?" "Duk suna lafiya suna gaishe ku." "Muna amsawa." Sai ta wuce ta dauki flask ta fita zuwa part din Baba, dama abinda ya shigo da ita kenan. Ko da ta koma jiya da daddare Baban ya kwanta, da safen nan kuma ba'a tada maganar ba, a ransa yaji babu dadin yadda tayi amma kuma ya mata uzuri sosai, tunda ko da Mama ce haka zatayi itama, tunda yanzu ko a hakan ne yasan akwai kalubale a gaba ma, shiyasa kawai ya bar maganar yaga abinda Allah zai yi. Ko da yaushe idan Ya Fauwaz ya shigo sai yayi mata maganar Ya Tariq, duk kusan rabin hirar su akan sa yake mata, yana sanar da ita duk kyawawan halayen sa, hakan ya saka ko bayan da ya tafi ta kasa mantawa da duk magangan da sukayi,ta dinga bitar su kamar wadda take bitar karatu [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (19) ***Kusan sati guda kenan da zuwan su Isma'il amma babu wani information daga wajen Jidda, sun yi waya da Safeera da sabuwar number ta amma ba wadda tayi wa wata maganar a cikin su, hakan ya kara tada hankalin Ismail ya samu Safeera da magaanar sai kawai ta bashi sabuwar number din Jiddan da bata so ta shiga abun nasu sosai azo a samu akasi tazo tana jin haushin Jiddah. Samun number ya dan rage masa damuwa ya koma daki ya kirata sai dai har ta gama ringing bata daga ba, tana chan kitchen tare da Aunty ta bar wayar a daki tunda dama babu me kiranta daga Amira sai baffan ta, sai kuma Safeera idan tana so tace mata tazo WhatsApp suyi hira. Sake kira yayi ya dinga jera kiran tunanin sa tana gani ba zata dauka bane dan shine, sai kuma wata zuciyar ta tuna masa ai bata da ma number dinshi bare taki dagawa saboda shi ne, shafa kansa yayi yana mata uzurin kila bata wajen yana kokarin hana waccan zuciyar tashi ta farko tasiri a tunanin sa. WhatsApp yayi login sai ya duba number din yaga tayi registering WhatsApp din sai kawai ya shiga kai ya tura mata kalamai masu dadi da sanyin gaske, hoping zata duba ta bashi time suyi magana ko da a wayar ne ba sai a fili ba. Cigaba da zama yayi rike da waya yana dakon kiran ta ko kuma zuwan ta online wanda yasan tabbas za'a yi dayan biyu, ko ta biyo kiran ko tazo online. Dakin ta shigo bayan sun gama aikin da Aunty, ta dan gaji dan abinci sukayi na mutane da yawa da za'a fita dashi waje duk da akwai masu aiki amma kuma ya zame musu jiki duk irin wannan aikin tare sukeyi da ita da aunty, kasancewar aunty zata je taga Baffa duk da bata fadawa Jidda in da zata din ba dan bata so tace zata shiyasa ta bar mata aikin ta cigaba da kula dashi ita kuma taje ta shirya, ta fito ita da Usman suka tafi tare da Driver. Gama aikin kenan an zuzzuba a manyan kuloli ta baro wajen tasan Abu zata karasa sauran aikin a fidda shi, wanka ta fara yi tana shiga dakin, ta maida doguwar rigar dake jikin ta mara nauyi sosai ta kwanta lamo tana jin kanta na dan sara mata, tasan alamun period dinta ne shiyasa duk take moody ga wata irin kasala da take ji, farko da bata gane ba sai da Safeera ta fada mata sannan ta ganar da ita duk abinda ya kamata ta gane ta sani. Pillow ta daga ta ciro wayar ta duba, missed calls din da ta gani rututu ya sakata saurin cire lock din sai taga bakuwar number, da saurin ta, ta kira number back dan tasan duk wanda zai kirata ya san tane sosai kuma irin wannan missed calls din da yawa sai kaji tsoron ko ba kalou ba. A firgice ya dau wayar da take ajiye da a saman chest dinsa yayi rigingine yana jiran kiran gashi yana da fita zai je ya samu Daddy a office dinsa amma duk sai yaji baya son fita kwata-kwata. Yadda yayi mata saving sunan haka ya bayyana akan allon wayar sa, ya daga ba tare da bata lokaci ba yana manna wayar a kunnen sa sannan yace "Bari na kiraki Jidda." Sai ya katse kiran, muryar sa tar a cikin kunnenta, bata kawo shi zai daga ba kwata-kwata, sai tayi sakalo da wayar sanda ta dauki burarin shigowar kiran nasa, ganin zata katse ya sakata katsewa ta dan karata kadan a gefen kunnen ta kamar me tsoron shocking tace "Assalamu alaikum." "Jidda ,wa alaikisalam. Ashe zaki daga." "Ina wuni?" "Lafiya lou, kina lafiya? Ya gida dasu Aunty?" "Alhamdulillah." "Ina kika shiga ne, aka bar wayar bawan Allah tana ta neman agaji." "Ina kitchen ne." "Ah kice dai ashe da babbar chef nake magana, shikenan kinga ni lafiya lou." "Uhum." Tace "Me kika dafa mana? Nazo na karba dan nasan zai yi bala'in dadi." "Abincin sadaka ne da akeyi." "Oh okh, next time sai ace muzo muyi tasting ko? Nasan komai kika dafa zai yi dadi sosai." Dan gajeren murmushi tayi me dan sauti, hakan ya sake bashi hope ya cigaba da zuba kamar be san yanayi ba, so yake dole sai yayi impressing dinta, ko ba komai a hankali zata saba dashi ta saki jikin ta dashi, shawarar da suka tsara kenan shi da zuciyar sa, ya fara kokarin saba mata da kanshi kafin komai ma yazo daga baya, duk maganganun da yake a gajarce take masa masa kanta na cigaba da tsananta mata da ciwo gashi bata so ta katse shi amma kuma maganar tashi ta ishe ta, sai da yayi ya gaji dan kansa sannan ya hakura yace zai kira anjima. Da sauri ta rigashi katse kiran ta kwanta tana tura kanta cikin filon ta yadda zata rage ganin hasken da yake kara mata ciwon kan. ***Ran Baba a bace yake sosai har Aunty ta gama masa bayani da abinda take so yayi idan Baba yazo masa da maganar Jidda, sai da ya bari ta gama tsaf sannan ya kalleta yace "Kin gama?" Sai a sannan taga yanayin fuskarsa, sai taji kamar an dake mata guiwowi, ta tabbatar ba zai goyi bayan ta ba kenan duk da yadda tayi ta kokarin tsara masa maganganun yadda zai fahimce ta "Kin bani mamaki Innajo, kin bani mamaki sosai." "Na'am?" "Yanzu har kece zaki budi baki kice na hana Alhaji auren Jidda? Kenan ma Jidda tana da wani uban bayan shi ban sani ba?" "Yaya baka fahimce ni ba." "Bana so na fahimce ki, ni ba butulu bane mara godiyar Allah, me Jidda tafi shi yaron da har zaki dage kai da fata? Wacece Jidda ma? Ke kina ganin ke da yar taki har kun kai wani matsayi da zaku yi abinda kuke so ko me?..." "Bari na tuna miki idan har ke kin manta, sanda Alhaji ya aure ki ke kanki kinsan ke ba sa'ar auren sa bace, haka yace yaji ya gani ya aure ki ya rufa miki asiri da ni kaina, sannan kika dauki yar taki da kike ganin karan ta ya kai tsaiko da har zaku butulce, kika kai masa ya karba ya rike babu banbanci da Yayan cikin sa, ko akwai banbanci?" Yace yana kafe ta da ido cikin bacin rai "A ah." Ta girgiza kai da sauri duk kwalla ta cika mata ido dan bata taba ganin bacin ran Baffa irin yau ba "Sannan karki manta adalcin Alhaji lokacin da ya rasa Muhammad, kina ganin idan wani mahaifin ne ba shikenan ba kuma maganar auren ku ma zata iya lalacewa akan haka, amma me yayi? Shine ma yake kokarin kwantar miki da hankali ya kuma hana uwar yaron nan yin wani yinkuri, wannan shine mutumin da kike kin dan sa kike ganin be dace da yarki ba tunda ita din yar gwal ce." "Dan Allah Baffa kayi hakuri, dan Allah." "Ki barni na gama tuna miki tunda ke kin manta, sanadiyyar waye na samu lafiyar kafata? Idan kin manta sai ki tuna, dan haka..." Ya nuna ta da yatsa "Jidda ba 'yata bace, haka kike ba taki bace, yar sa ce dan haka yana da damar yayi duk abinda yaga dama akan rayuwar Jidda, ke ko mutuwa nayi wallahi ba zan yafe muku ba idan kuka kiyi masa biyayya." "Dan Allah kayi hakuri Yaya, nayi laifi babba, amma dan Allah kayi hakuri." "Toh kar na sake jin wannan maganar kin daga ta, sannan idan kinsan kin bata masa rai saboda magaanar nan, lallai lallai ki bashi hakuri, sannan ita ma Jiddan zan saba mata idan har tace zata zo min da shashanci." "Ita bata ma san da maganar ba." "Idan ma ta sani din, kuma ko yanzu Alhaji yake so ayi auren sai anyi." "Allah ya huci zuciyar ka Yaya." "Amin." Yace a kufule, sum sum sum ta tashi ta fice zuwa gidan su Saude, daga nan bata wani jima ba tayi sallama ta tafi, dan da tasan ma abinda zai faru ne da bata zo ba, sai bayan Baffan ya karanta mata duk abubuwan da ta manta sannan ta dawo hankalin ta, tasan bata kyauta ba kuma dole zata bawa Baba hakuri akan maganar. ***Baba na zaune a hadadden falon sa na ciki wanda ke cike da ababen more rayuwa, news yake kalla hankalin sa baki daya yana kai har wayar sa ta gama ringing sam be ji ba. Mama ce tazo ta zauna a kubin sa, cikn shigar alfarma kamar ko da yaushe, kamshin turaren ta ya cika ilahirin falon. Dan juyowa yayi ya dube ta, yayi murmushi kawai itama ta maida masa ya cigaba da kallon news din har zuwa sanda aka gama, juyowa yayi ya dauki wayar sa zai yi kira sai yaga missed calls din Tariq, kwana wajen biyu kenan basuyi magana ba, yana taso ya kirashi dama yaji progress din training din nasa dan baki daya yayi dedicating lokacin sa akan son yayi achieving hours din nan, yawanci ma yanzu ya fiyi saboda yanayin busy din da yake shiyasa ya tsirga sosai duk da giant ne a tsaye yake amma hatta idanun sa sun fada saboda rashin isashen lokacin da baya samu. Ko waya ma da Baba kawai sukeyi shima kuma duk maganar akan training din nasa ne sai jefi-jefi yake kiran Mama ko ta kirashi yaga missed call ya kirata idan yana free. Yanzu ma fitowar sa kenan daga cikin wajen yana cike da farin cikin akwai yiwuwar in less than a year da ta rage masa sai iya hada hours din, shiyasa ya cika da murna ya kira Baba dan ya fada masa amma kuma be dauka ba. Cigaba da tafiya yayi zuwa in dai zai hau train dan yau akwai in da zashi ba kai tsaye gida zai koma ba, yana so yaje yayi siyayya kafin a shiga cikin sati ya zama so busy ya kasa siyan abubuwan da bashi dasu. Kiran Baban ne ya shigo, ya daga yana rataya rigar sanyin dake rike da a hannun sa a saman kafadar sa, suka gaisa ya tambaye shi yadda ake ciki, ya sanar masa da duk progress din da aka samu, yayi masa murna sannan yace yana so ya nemi alfarma a wajen sa "Inaso nayi maka wani katsalandan a rayuwar ka, duk da bazan fada maka ko menene ba, amma ina neman amincewar ka, idan har ka amince shikenan, ina me tabbatar maka da ba zakayi nadama ba." "Baba... Akwai abinda dama zakayi min da har sai an nemi amincewa ta?" "Eh." "Toh na amince Baba, iyaye ba zasu taba yin abu dan su cutar da dansu ba, sai dan su faranta masa, I can't wait na dawo nazo naga ko menene." "Masha Allah, thanks for trusting me, ba zaka taba dana sani ba, ka kula da kanka kaji? Sai munyi magana Allah yayi maka albarka." "Amin ya Allah." Yace yana jin dadi a duk lokacin da Baba ya saka masa albarka shiyasa yake yawan koyi da Baban dan halayen sa ababen koyi ne. Farin cikin sa ne ya karu bayan gama wayar, yana fatan ko menene Baban zai masa ya zame masa alkhairi a rayuwar sa. Duk abubuwan da yake bukata ya siyo ya dawo ya samu Ishaq yana kokarin knocking a kofar sa, sai gashi yazo, ya matsa ya bud'e masa ya shiga bayan ya rage mishi kayan dake hannun sa "Tuzuru ai na dauka ka dawo tun dazu ganin yau Friday da wuri kake dawowa." "Naje African market ne, na samo yan kayayyaki, dawowa ta kenan." "Ok naga alama ai, kaga da ka yarda kayi wuf da Yasmin duk wannan wahalar ba zaka sha ba, kuma ka samu cook." "Don't mention her name please." "Wai dai na tuna maka, kasan fa tana nan tana zaman jiran ka, wallahi da zaka yarda ko? Da har azumin nan sai ka daina shi, dama duk munsan dalilin azumin katon gauro kamar ka." Da sauri ya kalle shi, ya ajiye pack din pepper din da ya fito dashi yana maida hankalin sa wajen sa "Menene reason din fasting dina?" "Waye be sani ba, oga rashin aure ne zaka wani fake da busy busy baka samu kaci abinci." "Dan iska." Yace ya jefe shi da wani babban carrot, chafe wa yayi yaje wajen sink ya wanke yazo ya hau ci yana kyalkyalawa Tariq din dariya, murmushi kawai shima yake dan yasan maganar Ishaq din da kamshin gaskiya amma baya so yayi convincing kansa akan haka ne, dan be gama shiryawa aure yanzu ba, be ma fara neman matar da zai aura ba. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (20) ***Yana ajiye wayar Mama da take kallon sa tace "Me ake shiryawa ba'a sanar dani ba?" Murmushi ya sakar mata dan yana kyautata zaton idan ya fada mata zata iya bori ta tada hankalin kowa shi kansa Tariq din ta tayar masa da nasa "Wannan tsakanin uba da dansa ne." "Inyee, haka ne dama honourable?" "Toh idan kuna sirrin ku ke da yan matan ki ina sani ne?" "Ai shikenan, zamuji ai idan tayi tsami." "Ba ma zatayi ba in sha Allah." "Shikenan." Tace tana hasaso kila gida ne Babba Baban ya samawa Tariq din ko dai wani abun babba. Waya ya shiga yi ba kakkautawa, hakan ya saka Maman zamewa ta barshi shi kadai,ta koma dakin ta, ta dauki wayarta ta kira Aunty Mimi sukayi magana sannan ta fito ta nufi part din girls din nata, ta samesu kowacce tana zaune da waya ana fama, Maryam na karanta novel a arewabooks, ita kuma Umaima tana kan tiktok tana more kallo, Safiyya na waya da saurayin ta Dr sufyan (urologists ne). Sai jidda tana buga game din candy crush a sabuwar wayarta, shigowar Maman ya sakasu duk maida hankalin su kanta,kowa ya ajiye waya ta zauna tare dasu suka kunna TV suna kalla. Kusan 30min ta dauka a part din nasu, sannan ta tashi ta tafi, haka take musu kullum musamman idan Baba be shigo gida da wuri ba toh tana tare dasu har sai dare ya raba kafin ta tafi bangaren Baban. ***Duk yadda Isma'il yaso ya share amma ya kasa, ba sosai Jidda take hawa WhatsApp din ba ko yayi mata magana bata dubawa ma kwata-kwata, gashi ko kiran ta yayi sama-sama take amsa masa, shiryawa yayi kawai ya tafi gidan dan a kalla idan face-to-face ne zata saurare shi ko babu yawa, duk da yasan akwai yarinta a al'amarin ta, amma kuma ya san ta san komai, ya kamata ace ta bashi dama ko yaya ne. Haka kawai taji sam beyi mata ba ko kad'an, dan kiran da yake mata ma ba karamin takura mata yake ba, ji take kamar ta kashe wayar ta hakura gaba daya, dan da tasan Safeera zata bashi number da bata ma fara kiran ta da number din ba. Jujjuya wayar take a hannu suna zaune su biyu ita da Aunty kowa da abinda ya dame shi, ta lura tun zuwan Baba Auntyn bata da walwala har ya koma,sai dai kuma bayan da ta fita ranar ta dawo sai ta sake ganin sauyi sosai a tattare da ita dan hatta kuzarin ta sai da ya ragu, gashi bata ce mata komai ba balle tasan abinda yake damun ta. Knocking akayi a kofar, suka kalli juna ita da Aunty kafin ta tashi ta bud'e kofar, "Hajiya tayi bako." Sai ya juya Isma'il dake tsaye a bayan sa tun farko ya bayyana a gaban ta, da sauri ta janye kanta daga kofar cikin tafiyar sauri-sauri ta wuce falon zuwa bedroom dinta dan dan siririn mayafi ya saka ta yane kanta, jikinta sanye da riga me gajeren hannu da skirt. Tashi Aunty tayi ganin mutum a tsaye sai duk kunya ta kamata tace ya shigo ciki,ya shigo jikin sa a sanyaye, ya zauna sannan ya gaida Auntyn cike da girmamawa, ta amsa ranta duk babu dadi dan har ga Allah bata so Jidda ta rasa miji kamar Isma'il. "Bari a kawo maka ruwa." Tace tana neman hanyar barin falon, dakatar da ita yayi ta hanyar cewa "Aunty dan Allah a bar ruwan nan a koshe nake wallahi." "Toh shikenan, ina zuwa." Sai tabi bayan Jiddan, zuwa dakin Jiddan ta sameta a zaune a saman drawer ta zurma Hijab har k'asa fuskar ta babu fara'a ko kad'an, kallon ta Aunty tayi da ta gama gano bata son Isma'il din tun ranar farko tace "Kije kuyi magana, dan Allah ki saki ranki, Usman zaizo ya zauna." Dan sakin fuskar tayi, tayi gaba har ta fita Aunty ta kirata "Kina ji? Baka wulakanta mutum ko baka sansa Jiddah,kokari za'a yi a rabu lafiya, duk tsiya mutumin da yace yana son ka ai ya gama maka komai a duniya , kuma be kamata ya zama makiyi a wajen ka ba." Kara sakin fuskar tayi ta gid'a wa Aunty kai sannan tafita, maimakon ta tsaya a falon sai ta wuce shi ta fice ko kallon sa batayi ba, sai da taje ta riko hannun Usman sannan ta dawo falon, ta zaunar dashi a gefen ta, kanta a kasa ta gaishe shi, "Lafiya lou." Yace duk ya gama tsorata da yanayin ta. Shiru tayi tana taba botir din jikin rigar Usman, har lokacin bata yarda ya dago ba bare har su hada ido, kamar wanda aka tsoma a cikin ruwan zafi haka yake jin sa, ga wata iriyar fargaba da faduwar gaba, shi be taba samun kansa a irin wannan yanayin ba, baya iya komai sai tunanin ta, haka duk abinda yake ita yake gani, amma kuma zuciyar sa ta soma karaya ganin irin tarbar da ya samu daga wajen Jiddan a yau bayan ba haka ya santa ba "Jidda, maganar ranar nan ce tasa na sake dawowa, kinga ba zan hanaki karatun ki kawai dai inason a san dani ne, you can take all the time you want, ba zan taba magana ba, zan jira ki shiga university, idan ma har sai kin gama ne fine, zan iya jira." Banza tayi masa dan bata tsinci komai a maganganun sa ba, ita ba dan karatun ta, take kin sa ba, shi so halitta ne, haka kawai taji bata son shi so na soyayya, tana dai respecting dinsa a matsayin shi na Yayan Safeera. "Jidda baki ce komai ba, dan Allah say something, my heart is beating so fast, ba zan iya jure shirun ki ba, just say yes, ba zan sake takura miki ba, zan baki duk lokacin da kike so." Dagowa tayi, tayi masa kallon cikin ido, sai kawai shaidan ya hasaso mata shi da wani irin zumemen kai, wanda bata taba gani ba sai ranar, sauke kanta tayi da sauri ta hau girgiza kanta hawaye na biyo kuncin ta "Kayi hakuri ni dai." "Dan Allah Jiddah, ki taimaka min wallahi zan miki duk abinda kike so, idan ma bakya so na dinga miki magana zan daina, ni dai kar kice min a ah dan Allah." Cigaba da girgiza kanta ta dinga yi dan bata jin zata iya zaman aure inuwa daya dashi, be mata ba ko kad'an..ita kanta mamakin kanta take dan tasan idan banda fuskar ta da take da wani irin sihirtaccen kyau babu abinda zata nunawa Isma'il da har zata ki shi saboda shi. Kamar zai jamo kasa haka yayi, rabin jikin sa baya kan kujerar saboda tsabar dimuwar da ya shiga, “Ina son ki Jiddah, ina son ki fiye da yadda nake son kai na, dan Allah ki ceci rayuwata ki so ni ko da kwatan son da nake miki ne.” Ya furta bakin sa ararrabe yana rawa, shafe idanun ta, tayi da toka ta mike ta sungumi Usman tace “Kayi hakuri Ya Isma’il, ba zan iya ba, ba zan iya ba.” sai tayi gaba da sauri har da dan hadawa da gudun ta, daga muryar sa wadda take rawa yayi yace “Shikenan Jidda, shikenan sai watarana!” Amsa kuwwa karshen kalamen sa suka dinga mata a kunne, har ta dangana da bedroom dinta, in da ta bar aunty a zaune rike da wayarta tana kallon hotunan Tariq da suka kusa cinye dukkan gallery din, a yanayin da Jiddan ta shigo ya sakata dire wayar ta fita da sauri. Kansa a k'asa ya dora shi akan tafukan hannayen sa ta same shi, kiran sunan sa tayi a dan tsorace, ya dago idanun sa da suka rine sukayi masifar ja "Subhanallahi, Isma'il." Aunty tace ganin yadda idanun suka kad'a sukayi ja "Aunty Jidda bata so na, Jidda bata so na." Ya fada kamar wani zararre, sai ya mike yayi hanyar fita daga falon da sauri, Aunty ta kira shi amma yaki tsayawa, ya dinga sassarfa har ya dangana da wajen da yayi parking motar sa, ya shiga sai ya kasa kunna ta, hannun sa na wani irin kakkarwa, key din ne yafadi kasa, sai kawai ya kifa kansa akan sitiyarin motar yana jin wani irin makaki a makogwaron sa. He's shattered, be san ya zai yi ba, be san yadda ta ina zai fara ba, da kyar ya lalubo wayar sa, ya kira Farouk yace yazo ya tafi dashi, cikin kankanin lokaci yazo Nabil ya kawo shi, taimakawa Isma'il din sukayi ya koma baya ya zauna yana rintsa idanun sa da suke masa masifar zafi da zugi. Farouk ne ya ja motar Nabil ya bisu a baya. Washegari Baba yazo Kano, tare da wasu ministoci su uku, gaisuwa suka je sukayi sannan suka je wani kauye chan da aka samu matsalar bandits suka duba su suka kai musu tallafi, hanya ce ta biyo dasu ta garin su jiddah sai kawai Baba yace su tsaya garin su duba su. Baffa be san da zuwan su ba, dawowar sa kenan daga gona ana ta kokarin nome amfanin gona, wanka yayi ya chanja kayan jikin sa sababbi kasancewar juma'a ce yaje masallaci yayi sallah ya dawo ya zauna kofar gidan, kamar daga sama yaga motoci na nufo shi, ya tashi da sauri sanin waye yazo, dan tunda Baba ya samu mukamin nan be samu shigowa ba sai dai yana yawan waya da Baffan kuma yana masa aike akai akai dan hatta gidan sa an gyara masa shi sosai, ga kuma shago babba da Baban ya bude masa a chan kasuwa yana saida kayayyaki nan da nan yayi fes dashi kamar bashi ba. Dama iya Lami tunda taga ya dawo daidai ta daina rashin mutuncin ta dan tasan ba kamar da bane da tayi masa zai auna ta gaba, duk da haka bakin halin nata yana nan shi ma kuma ya sani sarai kawai yana rabuwa da ita ne. Tun kafin motacin su ta tsaya DSS din suka dire kowannen su fuskar nan a tamke, jama'ar gari da suka soma tururuwar zuwa gani su duk suka lallabe daga baya dan dama labari ya karade ko ina sai gashi kuma sun gani da idanun su. Dukkannin su mutane ne masu cike da kamala tamkar Baban, tarar su Baffa yayi cikin tsananin farin ciki gami da mamakin ganin su, suka gaisa a mutunce sannan yayi saurin shiga gida ya dauko babbar tabarma ya shinfida musu daga gaban gidan, suka zazzauna su kuma securities din suka tsaya daga gefe. "Alhaji sannun ku da hanya, wallahi ban yi tunanin zuwan ku ba,nayi mamaki matuka wallahi." "Hanya ce ta biyo damu Yaya, duk da dama lahadin nan na sa rai zamuzo da Alhaji Adamu da Malam Nura, sai kuma naga kawai tunda muna kusa mu karaso kawai." "Masha Allah, nagode nagode Allah ya saka da Alkhairi." "Amin Yaya, mun zo ne gaisuwa da kuma rokon iri, idan babu damuwa." Da sauri Baffa ya katse shi "Kar muyi haka da kai Alhaji, idan har akan maganar da Halima tazo min da ita ne akan Jiddah, toh babu ni a cikin wannan harkar, kaine mahaifin Jiddah bani ba, dan haka ba zaa tambaye ni amincewa ta akan Jiddah ba." "Yaya ba haka bane ,wai dama kaga..." "Alhaji kayi hakuri, amma kai ne mahaifin Jiddah, duk abinda ka yanke akan ta daidai ne." "Duk da haka da ka saurari honourable muji me zai ce." Daya daga ciki yayi maganar yana yabawa da dattakon Baffan "Toh ina jinku Alhaji, ni dai idan har akan maganar auren jidda ne da yayanta toh wallahi na amince, na bashi duniya da lahira, idan a shirye kuke ga mahaifin jidda nan a zaune (Ya nuna Baba) ku bashi sadakin Jidda a hannun shi, zan kira makwaftana tunda duk yan uwana basa raye a daura auren nan kafin ku bar wajen nan " "Yaya babu takura kuwa hakan?" "Babu ko daya Alhaji, idan ma har na bari kuka bar nan bamu gama magana ba ai anyi ba'a yi ba kenan bari Kuga." Sai ya mike ya zagaya bayan gidan, jim kadan sai gashi da mutane dattawa su shida, ya shiga yakaro wasu tabarmin sannan ya gabatar dasu a matsayin shaidu. Ba karamin mamaki su Baba sukayi ba, nan da nan cikin kankanin lokaci aka gabatar da komai, aka daura auren MUHAMMAD TARIQ NASIRUDDEEN DA HAUWA'U IBRAHIM JIMO, akan sadaki naira dubu dari. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (21) ***Alawa da goro aka raba sannan daya daga cikinsu yayi rabon kudi sosai, sannan suka bawa Baffa kudi masu dan kauri kafin suyi sallama su tafi, nan da nan labarin ya zagaye dukka kauyan. Zuciyar Baffa cike take da farin ciki mara misaltuwa, ya rasa in da zai tsoma kansa dan murna..Allah ya dube shi ya dubi maraicin Jidda yayi musu sauyi rayuwar da basu taba hasashe ba. Da magribar fari Baba ya shigo gidan, yadda yake cike da farin cikin abinda ya faru ba zai bari har sai Yaya tayi bacci ba sannan ya shigo gidan,shiyasa ya rage schedules dinsa ya barwa gobe. Dukkan lissafin YAYA akan wannan lahadin ne, Allah Allah tayi, satin ya zagayo amma sai ta ga yayi nisa sosai, gashi bata son a samu matsala komai kankantar ta, shiyasa take cike da wasi-wasin jiran zagayowar ranar. Idar da sallah magriba kenan da tayi, ta mike kafafunta da suke dan mata ciwo akan abun sallar, tana rike da tasbah tana ja lokaci zuwa lokaci tana daga kai ta kalli cikin dakin nata kamar me neman wani abu. Sallamar Baba ya sakata katse abinda take ta mike da dan saurin ta, ta fito falon tana son ta tabbatar shi d'in ne ko kuma dai muryar sa ce take mata gizo, shi din ne kuwa,nan da nan ta hau murnar ganin sa kamar wannan ne zuwan sa na farko wajenta saboda tsabar yadda ta cika da farin cikin ganin sa, tasan zai iya fasa zuwa wannan satin idan wani abun ya taso masa shiyasa take ta Allah Allah yazo. "Yaya irin wannan farin cikin duk na gani na ne?" Yace bayan sun gaisa ta kawo masa ruwa kamr ko da yaushe "Eh da murnar ganin naka ma, da kuma murnar na gama cire rai ba zaka zo wannan satin ba, kasan kuma alkawarin mu." "Yaya baki manta ba?" "Na manta kace? Tab!" "Toh Yaya albishirin ki." "Goro, fari kal kal." Ledar dake cike da goro da alawa ya mika mata gabanta, taja ta bud'e tana leka ciki "Me muka samu?" Ganin alawa da goro yasa ta kalli Baban da sauri "Ba dai aure kayi ba?" Darya ta bashi, yayi murmushi yace " A ah Yaya, goron auren Jiddah ne da Tariq." "Dan Allah! Kai kai kai kai Masha Allah, Masha Allahu, da gaske kake wai?" "Da gaske Yaya, mahaifin Jiddah mutumin kwarai ne,wallahi hanya ce ta bi damu, sai na gabatar masa da maganar,anan yayi tsalle ya dire sai dai ayi komai a gama, kuma fafur yace shi bazai karbi sadakin Jidda ba dan nine mahaifin ta, naji dadi kwarai da karramawar da yayi min, su kansu wadanda muka je tare tunda muka dauko hanya suke yaba masa." "Kai Alhamdulillahi, Abu kamar almara?" "Wallahi Yaya, kinga dai abinda Allah ya tsara, ko jiddan ba'a fara tuntuba da maganar ba, Allah yasa kar taga rashin kyautawarmu." "Ba dai Jidda ba, na gamsu da tarbiyyar ta, ko ma zaa bijire sai dai wanchan sahoramin, shima kuma be isa ba." "Haka ne." "Allah ubangiji ya saka muku da gidan aljanna, ka gama min komai a duniyar nan, Allah ya kare ka daga sharrin makiya, ya sa 'yayanka kai ma su rama maka, naji dadi nagode nagode." Sai ta fashe da kuka, kukan da ya saka Baba mikewa dan sarai yasan halin Yaya, yanzu sai ta rikice musu, "Amin Yaya, Amin Amin." Sai ya fice dan yana jin kukan nata har ya fara sauya salo, duk da kukan farin ciki ne amma yasan tsaf zata birkice tayi tayi tana farfado abubuwan da suka faru da irin fadi tashin da tayi dasu suna kanana musamman shi da zai iya cewa itace koman sa a rayuwa, ita ta tsaya masa har yayi karatun da a yanzu yake alfahari dashi. Waya yayan ta dauka bayan ta ajiye kayan a gefe, ta dinga dannawa tana kiran duk wanda hannun ta yazo kan number sa, tunda ita ba iya karatun tayi ba bare ta gane sunan waye, idan ka daga taji ba kai take nema ba sai kawai ta katse, haka tayi ta kira har tazo kan number Mama da tunda aka saka mata number ba su taba waya da ita ba,kowa dai yana da ta kowa ita Yaya Safwan ne ya saka mata a wayar. Mama na zaune bayan sun fito hutu daga wani taro na matan ministoci, suna zaune a wajen da aka tanadar domin hutawar su, suci abinci da sallah. Da la'asar aka fara taron da magriba tayi sai aka tafi hutun minti talatin sai a sake komawa zuwa isha a tashi. Hajiya huwaila ce a gefenta dama tunda tazo Abuja da ita suka fi sabawa sosai. wayarta ce ta shiga vibrating, ta ciro ta daga yar madaidaciyar jakarta, cike da mamaki take kallon number Yaya, dan bata taba kiran ta ba, bata kuma san akan dalilin da zai saka Yayan kiran ta ba sai dai idan tabbas ba lafiya, tashi tayi da dan saurin ta, ta fita daga wajen sannan ta daga kira "Assalamu alaikum." Kallon wayar Yaya tayi jin muryar ta, har zata kashe sai kuma taga ai ita tafi kowa chanchanta da taji wannan labarin, sai kawai ta amsa gaisuwar da take mata "Lafiya lou, ya yaran?" "Lafiya lou." "Kowa lafiya dai ko?" "Lafiya Alhamdulillah." "Toh Masha Allahu, kin samu labarin abun farin cikin da ya same mu ko?" " A ah Yaya, me ya faru?" " Batun auren Tariq da Jiddah mana, Alhaji be fada miki ba? Duk da dai ni dashi kadai mukayi maganar na kuma hane shi ko Tariq din kar ya soma fadawa har sai yazo da kafafun sa." Wata irin zufa ce ta shiga karyowa Mama, ta dinga jin kamar kunnenta be ji mata daidai ba, ta kasa bude baki bare ta amsa duk bayanin da Yayan take mata. Daina gane komai tayi har Yayan ta gama jawabin ta, ta kashe wayar. Wata kujera ce a gefen wajen ta karasa da sauri wajen ta zauna duk ta rikice "Auren Tariq da wannan figalalliyar yarinyar nan? Sannan a rasa wanda zai nemi shawarar ta? d'an ta data haifa a cikin ta, a rasa wanda zai nemi shawarta saboda tsabar karfin hali da nuna iko. Sai yau ta kara tabbatar wa Yaya bata son ta, haka kuma bata son yayan da ta haifa, dan idan har tana son Tariq ba zata taba masa irin wannan auren ba, kamar wani karamin yaro ace har Tariq zaa iya irin wannan auren? Lallai duk wanda ya shirya wannan be so zaman lafiya ba, ko waye kuwa. Tsanar aunty ce ta kara karuwa sosai a zuciyar ta, dan tasan tabbas da saka hannun ta aka kakabawa Tariq munafukar yarinyar me zubin yunwa. Tunanin ta ne ya kawo mata wayar da taji Baban nayi da Tariq, wato dama abinda yake nufi kenan, shine suka boye mata dan kar ta hana, lallai kuwa dole ne ta nunawa Baban itama tana da iko akan Tariq dan ba shi kadai ya haife shi ba. Kasa zama tayi a karasa event din, ta fice bayan ta nemi ayi mata afuwa saboda tasowar wani babban al'amari. Tun a hanya take jerawa Baban kira amma be dauka ba, kira ta cigaba da yi dan bata jin idan har be dauki wayar ta ba zata iya zama bata je ta same shi ba. Har ta karasa gidan be dauka ba, ta shiga yaran duk suka tashi suna kallon yanayin ta, zare dankwalin kanta tayi ta jefar da jakar hannun ta da Amira take shirin karba, "Wallahi ba zai yiwu ba, ni za'a cutar saboda an ga sanda Muhammad ya mutu nayi hakuri, shine yanzu saboda tsabar wulakanci za'a yiwa Tariq irin wannan wulakantaccen auren, wallahi ba zai yiwu ba." "Mama please calm down, menene ya faru?" Safiyya tace tana rike hannun Maman, ta taimaka mata ta zauna a daya daga cikin kujerun falon, Maryam tayi sauri ta kawo mata ruwa ta zuba mata a cup ta mika mata, tasha kad'an ta ture ranta idan yayi dubu ya baci, ba dan dare ba a yau zata dira Kano wallahi, amma duk da haka da asubah zata dirar musu wannan karon ba zata kyale ba. "Dan Allah Mama me faru? Wanne irin aure akayi ma Ya Tariq din?" "Wai yanzu Safiyya ya rasa yarinyar da za'a hada Tariq da ita sai figaggiiyar yarinyar nan Jidda, saboda tsabar Yaya bata so na, shine aka hada aka rufe min." "Jidda kuma Mama?" "Eh." "Amma waya fada miki Mama? Ko dai an samu misunderstanding dan yanzu muka gama magana da jiddan a WhatsApp kuma bata fada min ba." "Kakarku ce da kanta ta kirani, ko muna yar wasa da ita bare nace wasa take min." "Toh Jiddan ma bata sani ba Mama." "Dallah rufe min baki, idan ma ta sani dole ne ta fada miki? Mutanen da suke munafukai, wato abinda ya faru da mahaifin ku shine shima Tariq aka kakaba masa ita, wallahi toh ba zata sabu ba, sai sun warware auren nan idan har ni na haifi Tariq a cikin ciki na." "Kiyi hakuri yanzu dai mama ,ki tuntubi Ya Tariq din ko shi yace yana so, kar azo kuma a samu matsala." "Wanne Tariq din? Lallai ma, Tariq ne zai so yarinyar nan,amma bansan ma baki da hankali ba sai yau, Tariq ba zai taba son mace irin ta ba, ni kawai suke so su bakantawa, a aure min miji a aure min d'a." "Kiyi hakuri toh." Mikewa tayi, ta shiga kwalawa Atika me aiki kira, tazo a sukwane dan daga jin kiran Maman a fusace take, ta nuna mata abinda zata biyo ta dashi, tayi gaba ta bita da sauri su kuma sukayi tsaye har sai da suka ga shigewar ta sannan suka hau yar rige-rigen daukar waya,Yaya Maryam ta kira ita kuma Amira ta kira Jidda, Umaima kuma ya Safwan ta shiga kira, daki Safiyya ta tafi kawai ba tare da tace komai ba. Yaya ce ta fara dagawa dan gama wayar ta kenan da ya Safwan da ta samo shi garin kiraye kirayen ta "Waye?" Tace tana dagawa "Maryam ce Hajiya Yaya" "Hala kin samu labari ne shine kika bugu min kiyi tsegumi." "Kai Yaya, kiranki nayi fa na gaishe ki." "Munafuka,nasan me kika kira kiji, aure aka daurawa yayan ku, kuma duk me dogon bakin da ta fada masa sai nazo har Habujan na tattaka ta." "A jirgi zaki zo ko?" Tace tana kunshe dariyar ta "A uwar jirgi zanzo." Dariya ta kyalkyale da, dan duk sun san yadda Yaya take bala'in tsoron jirgi, katse kiran tayi tana jan tsaki, sai kuma ta tuna ai yau ranar farin cikin ta ce b zata bari su bata mata ba. ***Kamar yadda Baba ya jewa Yaya da maganar haka ya jewa aunty, ta shiga shock sosai amma sai ta nunawa Baban ba komai, ta kuma bashi hakuri akan abinda ya faru satin da ya wuce, yaji dadi har ya saka mata albarka, tace zata fadawa jidda yace ta kira masa ita shi da kansa zai fada mata, zuwa tayi kiran jiddan ta sameta rike ta waya a tsaye tsakiyar falon, tana ganin Aunty tayi wajen ta da sauri "Aunty wai haka ne?" "Me?" Tace tana kallon yadda duk ta birkice "Amira ce ta kirani." "Zo ki zauna." Tace tana jan hannun ta,suka zauna sannan tace "Gaske ne jiddah,yadda kika ji maganar haka nima na ji ta yanzu, duk da tun satin da ya wuce naji maganar shine har kika ga na fita ranar juma'a, toh ba in da naje illah wajen Baffa, na sameshi da maganar, kinsan me ya faru? "A ah.". Ta girgiza kanta da sauri "Kaca-kaca yayi min, ya kuma tabbatar min da be yafe mana ba daga ni har ke idan muka bijire wa Baba. Har ga Allah naso ki da Isma'il, sai dai kinga ba mijin ki bane, shiyasa ma Allah be saka miki son shi ba, kiyi hakuri dan Allah karki ki yi musu biyayya, domin iyaye sun fi gaban nan, ina me tabbatar miki zaki ga haske da budi a rayuwarki " Kanta a k'asa, hawaye ya shiga bin fuskarta, bata san a wanne yanayi take jin zuciya da gangar jikin ta ba, sai dai tana jin wani irin yanayi mara misaltuwa, itace aka daura wa aure? "Tashi ki share hawayen ki, Baba yana son magana dake." Da sauri ta shiga goge hawayen da bata san ainahin na menene ma ba, ta mike tabi bayan aunty zuwa bangaren Baban, suka shiga da sallama ya amsa yana kallon Jiddan da kanta yake a kasa tausayin ta na kamashi ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (22) ***A k'asa ta zauna daga farkon falon, Aunty kuma ta zauna daga gefen Baban, kallon tausayi yake wa Jiddan dan sai da ya gama kallon ta sosai sannan ya shiga bayani cikin salon da yasan zai wanke kansa ya kuma wanke Baffa, sannan ya samu ta karbi abinda suka zo mata dashi, nasiha sosai yayi mata akan rayuwa sannan ya kawo maganar auren, wanda ya sakata jin Abu ya tsirga mata tun daga sama har k'asan kafafunta, ta kalmashe kafar cikin son rage abinda take ji din duk da bata san menene ba. Dukkan maganganun da Baban ya fada mata sun yi matukar tasiri a gareta, ba zata iya taba kin Ya Tariq ba, tunda har ya fito daga tsatson Baba, mutumin da yake da girma da k'ima a idanun ta. Tana kyautata masa zato, tana fatan yayi halin Baban ko da ba dukka ba. Maimakon ta koma dakin ta, sai tayi bangaren Yaya dan tasan idan ta keba kanta toh dole tunane tunane zatayi tayi, gwara tazo ko ta rage daren. ***Tunda suka bar kofar gidan su Jidda yake kwance a dakin Farouk, kamar wanda ruwa ya cinye haka yake ta kwanciya, babu abinda ya saka acikin sa, sai wani irin suya da kirjin sa yake, babu yadda Farouk be yi dashi ba, akan ya saka ko da wani abu ne a cikin sa, amma yaki sam. Sallah ma da kyar ya tashi ya hada azahar da la'asar haka magriba da Isha. Kansa na tsakankanin kafafuwansa bayan ya idar da sallar Farouk ya sake shigowa, ya dube shi a in da yake zaune ya girgiza kai,ya kira sunan shi, be amsa ba sai dagowa da yayi ya kalle shi "Bro dan Allah man up mana, ka tashi muje wajen Safeera muyi mata magana, may be ta iya convincing Jiddan, ni nayi mamaki ma wallahi, na zata kace bata da saurayi ko?" "It's too late, Jidda bata so na, nasan kuma ko shekara dubu zan bata ba zata taba so na ba, na gani a cikin idon ta. Dama nayi ma kaina alkawari idan har tayi rejecting dina ba zan takura mata ba, zan hakura da ita. You can't force anyone to love you." "Amma kuma you can try your best to win their heart, kayi saurin given up." "Ba zaka gane ba, inaji a raina ba zan iya cigaba da rokonta ba, har kusan kasa na kai ina rokon ta, and she said no, me kake so nayi?" "Fight for your love mana, don't be a looser, ka bata time ta kara tunani sosai, dama kamar kayi rushing abun, kaga fa akwai yarinta akan su, kila ma bata san menene soyayya ba, she's just nervous." "Kasan kiyayya? Ita na gani a cikin idanun jidda, na hakura, bata so na ba zata kuma taba so na ba." "Shikenan, Allah ya mana zabin alkhairi, karka wahalar da kanka toh, eat something, kalli yadda ka koma, mom ta kira wayar ka na daga nasan tana jiran ka." "Muje ka sauke ni, ba zan iya cin komai ba." "Ko tea ne kasha dan Allah " "Zan sha idan na koma." "Ok muje toh." Hannu ya mika masa ya tashi, yayi kamar zai fasi sai da Farouk ya tallafe shi, sannan ya taimaka masa zuwan wajen motar. ***Yadda Mama taga rana haka taga dare, kamr ta jawo gari ya waye haka taji. Ana idar da sallah aka kaita airport ita da Safiyya sai securities biyu, kafin tara tana Kano, kai tsaye doshi part din Baban lokacin ko tashi be ba, Aunty na falon tana hade masa wasu takardu waje daya, knocking akayi, ta tsaya da abinda take cike da mamakin wanda zai knocking a part din Baban dan ko Usman baya biyo ta bare tace shi ne. Wajen kofar taje ta dan leka ta jikin dan opening din dake jikin kofar bata ga kowa ba, sai tace waye "Matar gidan ce." Rass! Gaban ta yafadi jin muryar Maman, ta tabbata ba zuwan lafiya bane musamman da tunda tatafi idan ba sallah ba, babu abinda yake kawo ta, murda key din tayi ta bude kofar, ta matsa baya da sauri ta shigo ciki. "Sannu da zuwa." Tace ganin tana mata kallon sama da kasa, bata amsa ba, sai jan dogon tsaki da tayi cikin bacin rai tace "Munafuka algunguma, muguwa maci amana, saboda ke bakar makira ce, shine kika san yadda kika yi, kika shiga kika fita kika sa aka kakabawa Tariq gwanjon yarki, bayan yadda kika kakabawa mahaifin su kula.da ita, wato dan ina kyale abubuwa ina dauke ido shine har kika samu damar hada wannan shirmammen auren wanda bashi da maraba da auren gangan a waje na." "Haba Maman Fauwaz, kamar yadda kika ji labarin auren nan wallahi haka naji, bani na hada ba, Yaya ce ta hada kuma nima kaina ba wai inaso bane." "Dallah rufe mana baki, ai ke babu kalar munafuncin ki da ban sani ba,zanzo kanki bari na gama da shi." Sai tayi fuuu ta bude bedroom din Baban ta shiga. Zuciyar Aunty ce ta shiga yi mata zafi, ta gaji ta gaji da cin kashin da aunty take mata, ta gaji da tozarcin ta, tana kyale ta ne ba wai dan tana tsoron ta ba, sai duk dan a zauna lafiya, ta amsa tayi laifi a lokacin da ta auri Baba amma ya zatayi da kaddararta? Shikenan ace abu yaki ci yaki cinyewa? Ta kai karshe a wannan karon sai dai duk abinda zatayi tayi amma ta daina bin ta. Kin fita tayi daga dakin kamar yadda take yi a baya, ta cigaba da aikin da take tana jiyo hayaniyar Maman sama-sama. **Tunda ta shiga dakin ta saka Baba a gaba tana banbanmi, me kulata ba, yana jinta duk abinda zata fada ta fada aure dai ya riga ya dauro, kuma tunda har Jidda ta amsa masa da ta amince shikenan, bashi da matsala da kowa dan yayi wa Yaya abinda take so. Duk yadda Mama taso tunzurashi sam yaki bata hadin kai, cigaba da danna wayar sa yayi rabin hankalin sa na kanta rabi na wayar. Kamar kunnen sa ne yake masa gizo sanda yaji maman na cewa "Duk wadda ta tsara hada auren nan wallahi ban yafe ba, ko wacece ta cuce ni." Sai ta fashe da kuka ganin Baban ya ki kulata, saukar mari taji akan fuskar ta, baban dake tsaye yana huci a gabanta ya nuna ta da dan yatsa "Duk abinda zaki fada a kaina ko kan mahaifin jidda ko Halima ko ita Jiddan duk ki fada ba zan hanaki ba, amma a hir dinki kika sake sako mahaifiyata, dan dukkanku albarkacin ta kuke ci, kuma wallahi wallahi wallahi, kinji na rantse ko? Idan har kika ce zaki daga min hankali akan dan na yiwa Tariq aure, wallahi sai na nuna miki kuskuren ki,kuma ko da wasa kika kira Tariq ko kika saka yaran nan suka kirashi da maganar wallahi sai mun samu babbar matsala." "Naga sam baki san kaddara ba, ba kuma ki isa ki ce zaki fadi magana akan Yaya ba, baki isa ba wallahi." Wajen da ya mareta, ta rike cike da tsananin mamaki, tunda suke da Baba, be taba ko da daga mata murya ba, bare har yakai ga taba lafiyar jikin ta,komai take so tun daga zamanin kuruciya har gobe shi yake mata Ko kwakkwaran motsi ta kasa yi daga wajen da take tsaye, ta san shi sarai bashi da sauki idan har yayi fushi, bare fushi irin wannan da bata taba ganin yayi ba. Ficewa yayi ya barta a dakin,ya samu Aunty a falo ganin yanayin sa ya sakata yin shiru dan da har zatayi magana, har ya kai kofa sai ya juyo yace. "Ku fara shirye-shiryen tarewar ku a wannan satin." Daga haka ya saka kai ya fice, be jira yaji ko ta amsa ko bata amsa ba. Kasa fitowa Mama tayi daga dakin saboda tsabar kunya, a mareka kishiya tana ji ai ba karamin zubar maka da mutunci bane, a tunanin ta Auntyn zata fita bayan Baban ya tafi, taji shiru shiru, sai kawai ta yanke shawarar fitowa, ta fice fuuu, bata ko dubi part din Yaya ba, ta fada mota, dan dama a chan main house dinsu aka sauke Safiyya, saboda haka chan ta koma, ta samu Hajiya Babba da maganar, da duk abinda ya faru da abinda Baban yace, shawara ta bata akan ta bar komai har zuwa dawowar Tariq din, dan suna da yakinin ba zai taba amincewa ba. Da daddare suka koma, ta tattaro su ta fada musu abinda Baba yace akan maganar fadawa Tariq din, dama Safiyya da Fauwaz ne kawai suke magana dashi, kuma wajen kwana uku kenan ma basu yi magana ba, dama kuma Fauwaz ba zai fada ba dama Safiyya ce itama tunda aka yi maganar ba zata fada ba. ***Mom na zaune a falo Isma'il ya shigo, yana tafiya kamar wanda zai fadi, "Innalillahi, me faru?" Tace tana yin wajen sa, a cikin kujerun falon ya zauna yana jujjuya kansa da yake masa wani irin mahaukacin ciwo, Safeera dake kan dinning tana dinner ta taso da sauri, tazo ta durkusa a gabansa tana tambayar "Ya Isma'il me ya same ka?" Da kyar ya bude bakin sa, da yayi masa nauyi yace "Jiddaaa." "Me ya samu Jiddan?" "Ba...ta..so..na." ya fada a rarrabe saboda tsabar yadda yake ji, ga yunwa da ta hadar masa ta sake taimakawa wajen rashin kuzarin sa. "Kirawo min Dr Aminu Safeera, yi sauri yazo ya duba shi, wannan abu har ina, dama wallahi kamar nasan za'a yi haka, naji tsoron ganin yadda kake son yarinyar nan, kalle ka yau daya Ismail, akan soyayya ka koma kamar wanda yayi jinyar shekaru?" Jujjuya kansa yake, Safeera ta kirashi ta dawo gaban Ya Isma'il din cike da tausayin sa, ita kanta ta hango faruwar hakan dan tasan Jidda, tasan idan har bata son shi ba zata taba barin shi yayi ta fama ba, zata fada miki ne kai tsaye, sannan kuma ba zata taba sauya raayinta ba. ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (23) ***Kafin isowar Dr Aminu, zazzabi me zafin gaske ya rufe shi, sai rawar sanyi yake saida aka kashe AC falon da duk wata na'urar sanyi me alaka da wajen, daki ya taimaka masa ya kaishi ya kwanta,sannan ya hau examining nashi, ya gama ya rubuta masa magani sannan ya daura masa drip saboda yadda jikin sa yayi weak gashi babu komai da ya saka a cikin sa, fita yayi yaje ya kawo magungunan yace a bashi idan ya tashi ya sha, sannan yayi musu sallama ya tafi. Jigum sukayi a dakin nasa cikin yanayin rashin jin dadi har Daddy ya dawo ya same su. Baya hada yaransa da kowa da komai, shiyasa Mom na kiran sa ya taho gidan ba dan ya gama abinda yake yi din ba, a dakin suka tare gaba daya sai Safeera ce da ta soma jin bacci mom tace taje ta kwanta. Dakin ta, ta shiga maimakon ta kwanta sai ta dauki wayarta duk da kusan sha daya na dare ne, ta kira Jiddah wadda take kwance tana ta juye-juye, tana ganin kiran taki dagawa dan bata san me Safeeran zata ce ba haka itama bata san amsar da zata bata ba. Da safe ya tashi da dan kwarin jikinsa saboda drip din da yasha, Daddy ya gani a dakin yana kallon sa, ya taso da sauri yazo gaban gadon nasa, "Isma'il, ya jikin naka?" Yace ba tare da yasan dalilin ciwon nasa ba dan Mom bata fada masa ba, dan yatsine fuska yayi kadan sannan yace "Naji sauki Daddy." "Toh Allah yakara sauki, bari naje na shirya, ka tashi kayi sallah, sai a kawo maka breakfast saboda ka kara samun kwarin jikin naka, zazzabi bashi da dadi." "Tohm, dan Allah amma Daddy inaso na tambaye ka wani abu." "Ina jinka." Ya tsaya da shirin barin dakin da yake "So nake a matso da tafiyar karatun nan, ko cikin next week ne." "Me yasa? Da kace baka shirya ba, an samu change of plan ne ko me?" "Eh Daddy, yanzu inaso natafi,as soon as possible, please Daddy." "Ok, ba damuwa ka bari ka kara samun sauki, sai muyi maganar fixing date din." "Ai na warke, please Daddy." "Shikenan, ka same ni a falo idan ka gama." "Nagode." Tapping bayan sa yayi, ya fita shi kuma ya fada toilet. Tun last two months Daddy yake masa maganar masters da zai fara, ya dinga jan abun saboda ya samu Jidda idan yaso suka daidai ta, sai ya tafi tunda ba yawa just two years ne be ma kai ba, har yaje ya dawo lokacin ta shiga university ta fara karatun ta itama, that was his plan, sai gashi komai ya ruguje a cikin yan awowin da ba su gaza ishirin da hudu ba. Ganin haka ya saka shi yanke shawarar tafiya kawai tunda hatta admission yana dashi a hannu da komai, visa kawai zai yi applying wadda yake saka ran in a week ma zata zama ready, babu amfanin zaman sa tunda har Jidda ta k'i shi, bashi da amfanin cigaba da zama gwara yaje ya amfani lokacin da yake dashi. ***Duk da Jidda taga kiran Safeera kuma ta sake gani ma da safe amma ta kasa kiran ta, bata so ko kad'an su samu matsaala, ta san kuma d'aga wayarta a lokacin zai iya zama matsala tunda ta san a yadda Ya Isma'il ya fita ta kuma tabbatar da sun san abinda ya faru. Aunty ce ta shigo daga part din Baba, ta zauna tana sauke ajiyar zuciya, a yanayin da taga Mama zata iya komai dan ganin auren nan ya baci, bata so jiddah ta shiga matsala ko kad'an musamman a irin wannan karancin shekarun nata, dama dai duk abinda ta guda kenan, dan dai su iyaye maza basa bawa ire-iren wadannan abubuwan muhimmanci ko kadan, tayi mamaki da har Maman ta dauko kafa tazo, har kuma suka samu sabani da Baba akan hakan wanda ko lokacin aurenta da Baban basu samu irin wannan matsalar ba dan Mama mutum ce me matukar kissa da iya takunta a wajen Baban dan duk wuya bata taba bari yaga aibun ta, amma kuma a yadda ta kasa dauke idon ta akan wannan auren ne ya sakata sake tsorota da lamarin. Wayar Jidda ce ta sake kara a karo na uku tun shigowar aunty, ta kalle ta cikin son neman karin bayani tace "Ki daga mana ana ta kiranki kina ji." Yadda Auntyn tayi sounding yasa ta gane ranta a bace yake, daga wayar tayi sannan tace "Hello Safeera." Wani kallo Aunty tayi mata, sai ta tashi sum-sum-sum ta bar falon zuwa dakin ta, girgiza kai kawai Aunty tayi,ta shige daki itama ta hau tunanin yadda zasu fara hada kayayyakin da zasu bukata a chan din dan ba komai zasu dauka ba. ***Shiru jiddah tayi tana sauraron banbamin masifar da Safeera take akan kin daga wayarta bayan tasan dole ne ta kira ta, sai da ta gama tas duk da bata sako maganar Isma'il din ba sannan tayi shiru Jiddan ta bata hakuri "Bana kusa da wayar ne, kiyi hakuri." "Ko dai kika ki dagawa ba, kar nayi miki maganar Ya Isma'il." "Ba haka bane ba fa." "Toh me? Ni dai ban ce miki dole ki so shi ba, babu dole ai a soyayya, dama kiran ki nayi muyi wata magana amma shikenan." Ta wayance kawai dan bata ga amfanin dawo da maganar baya ba, ita da kanta Jiddan idan taga ta share zancen zata saki jikinta har ta bata labarin abinda ya faru. "Dan Allah fada min, wacce maganar ce?" "Ah ai kuma shikenan, idan kin matsu kina so kiji ki kirani da kanki." "Toh zan kiraki, kinsan me ya faru? I'm clueless gaba daya, bansan ma wanne irin tunani zan ba." "Oya,tell me ina jinki." "Uhm... Jiya aka daura min aure." "Wait what!!!" Ta fada da dan karfi dan yadda maganar tayi shocking dinta "Kamar ya? Ban gane ba, aure kuma, da wa?." "Ya Tariiiiq." Dip Safeera ta dauke wuta, kamar bata kan wayar, sai da ta ja wasu yan sakanni sannan tace "Yanzu dama all this while jidda kinsan yayanki za'a aura miki amma kika ki fada min,haka kika dauki friendships dinmu? Baki yi trusting dina ba ko? Shikenan nagode." Ai kafin Jiddah tayi magana ta katse kiran, ta kalli wayar ta girgiza kai kawai, me neman kuka ce dama aka jefe ta da kashin awakai, dama zuciyar Safeern a kusa take da abinda ya faru tsakanin su da Ya Isma'il, sai kuma katsaham tace mata an daura mata aure bayan dah tana dan da hope din ko aka kara turawa Ya Isma'il din ya samu kanta, duk da tasan Jidda kaifi daya ce tun basu kai yanzu ba,idan tace yes toh babu abinda zai sakata dawowa tace no, haka ma vice versa. Sanin cewa sarai ko ta kirata ba zata daga ba, ya sakata tura mata sakon text message, tayi mata bayanin abinda ya faru a takaice, ta ajiye wayar daidai lokacin Aunty ta kwalo mata kira, da saurin ta, ta amsa ta fita dan ta lura sarai Auntyn a wuya take akan maganar auren nan. A daki ta sameta ta fito da kayan wardrobe dinta gaba daya, tana ware su,zama Jiddan tayi ta shiga tayata, anan take fada mata maganar tafiyar, shiru tayi dan bata kuma san kalar sabuwar rayuwar da zasu fada ba, tun bayan komawar Maman Abuja aunty ta samu yancin kanta, bata da wata damuwa dan idan ba sallah da akayi ba suka zo babu wani abu da yake hada su waje daya, shima har a gama hutun sallar su tattara su koma ba wani zama Maman take a gidan ba,kullum cikin fita take.l shiyasa yanzu take hasaso irin zaman da za'a yi, gata kuma, wanne irin tarbar Maman zata yi mata? Shin zata taba karbar ta kuwa a matsayin matar Baban danta? Toh wai me da sanin ta kuwa akayi auren nan? Sai ta tuna da sunan bararojin da ta taba kiran ta dashi cikin son nuna kaskancin ta, ajiyar zuciya ta sauke, dan tasan tabbas akwai kalubale babba a gabanta, amma koma menene tana rokon Allah ya duba ta, ya kawo mata sauki. Suna aikin Aunty na kokarin nuna mata rayuwa da kalubalen da yake cikin rayuwar aure, taana ji tana kuma daukar komai a kanta, har suka kammala aikin taje ta zuba abinci ta koma dakin ta, taci sannan itama ta hau ware kayan nata, tana daukar wanda zata bukata ta. Hakan ya jata har yamma dan sai da ta hada komai kaf dan zataje tayi kwana biyu a gidan su kafin ranar tafiyar da zata dawo ana I gobe. Sai da ta gama tas sannan ta dauki wayarta, taga reply din safeera, tayi murmushi kawai ta sake tura mata wani, _"Wednesday zamu koma Abuja."_ Sakon na shiga ta biyo shi da kira, ta dauka tana murmushi dan tasan wata masifar ce "Nima wallahi dazu na san da tafiyar." Tayi saurin cewa tana dariya "Allah Jidda ko? Yanzu dan Allah shikenan tafiya zakiyi ki barni? Ni kadai ga Ya Isma'il shima tafiya zai,haba dan Allah." "Zamu zo sallah fa, ko weekend nasan ba wai mun tafi gaba daya bane, ni ma ba son tafiyar nake ba, kinga achan zamu fara school ni da Amira shiyasa ma." "Ai shikenan, zan shigo gobe." "Ok Allah ya kaimu, sai kinzo." "Amin, bye." "Bye." Maimakon ta ajiye wayar sai ta samu kanta da shiga photos din wayar, ta bude hotunan sa, tana dubawa,tana tuna wai mijin tane,an daura musu aure, bata san me take ji game da hakan ba, kawai tasan tana jin ta at ease, bata da wata damuwa ko fargaba a zuciyar ta. Ba kamar idan taga Isma'il ba, ba kuma kamar ace Isma'il aka aura mata ba, ta tabbatar zata iya bori akan hakan. Ya Fauwaz ne ya kirata, tana dagawa ya hau yi mata kirari "Kaga amaryar Ya Tariq, kaga amaryar Captain Tariq, kaga amaryar international pilot, eh Masha Allah, ban taba ganin perfect couples irin ku ba, kun yi matukar dacewa, da za'a bada award za'a iya baku award din perfect couples of the year." Dariya take tunda yafara maganar, "Kai Ya Fauwaz." Tace farin ciki na mamaye zuciyar ta " Allah da gaske Jiddo, auw Aunty Jidda." "Na shiga uku, nice Auntyn?" "Emana, kin zama matar Big B, ai dole ace miki Aunty." "Kai dai Ya Fauwaz ka iya tsokana wallahi." "Allah ba tsokana bace, da gaske nake. Har Allah, Allah nake ya Tariq ya dawo yaga amaryar sa, nasan ji zai yi kamar an tsunduma shi a aljanna." "Hum umm." Tace tana giggling "Toh ya ake ciki?" "Alhamdulillah wallahi." "Toh Masha Allah, dama nace bari na kira matar yaya, kar ya dawo yace mun bar masa mata babu kulawa." "Ya Fauwaz ko?" "Na barki lafiya toh." "Nagode." Wani irin dadi ne ya rufe ta, dan ba karamin dadin kalaman Fauwaz taji ba, ya bata kwarin guiwa sosai wanda har ta soma hasaso rayuwar ta anan gaba kad'an. Murmushi tayi tana lumshe idanun ta, ta furta a hankali.. Matar Ya Tariq ***Washegari da wuri Safeera tazo, suka shige daki suka shiga hira, har kusan azahar sannan ta je ta kawo musu abinci suka ci sukayi sallah, sannan Safeeran tace zata tafi dan Mom ma da kyar ta barta tazo dan dai tana son duk abinda suke so ne, mayafi ta yafa ta rakota gate in da driver gidan su yake jiranta. Hakurin abinda ya faru tsakanin ta da Ya Isma'il ta bata dan duk yadda taso dauko maganar da suna ciki Safeeran taki yarda da ta dauko maganar sai ta goce da ta sake daukowa sai ta shashantar da maganar ko ta nuna bata ma ji ba. Yanzun ma tsaki tayi kawai ta harare ta,ta shige mota. Part din Yaya ta wuce ta sameta kafarta na mata ciwo, ta dauko maganin da ake shafa mata, ta shafa mata a kafar sannn ta zauna tana rage mata zaman kadaitar. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (24) ***Kwanan ta biyu a gidansu, Baffa yayi mata nasiha da kashedi sosai akan abinda ya faru, ya kuma ja mata kunne sosai akan kar yaji kar ya gani, duk a tunanin sa zata bijire, be san da gaske take son abun. Wuni tayi ranar da tazo a gidan Saude wadda akayi bikin ta da kaka, bata samu zuwa ba lokacin suna examz, gashi hadda tsohon cikin ta, sun sha hira suka tuna da sannan ta dawo da la'asar sakaliya. Iya Lami nata haba-haba da ita,ta share ta kamar bata san Allah yayi ruwan ta a gidan ba, dan ko kad'an bata son matar dan babu kalar azabar da bata gana mata ba, akwai wani duka da tayi mata har yanzu da ragowar shatin dukan a gadon bayan ta abunka da fara. Shiyasa taki sakin jiki da ita sam bare ma su zauna suyi doguwar magana. Ranar da zata tafi Aunty ta turo aka dauketa, dan ta karasa abubuwan da bata karasa, dan da safe zasu tafi washegari. A tsakar gidan Yaya ta tarar dasu ana ta fama da Yaya tayi tsalle ta dire babu shegen da zai sakata shiga jirgi, idan kuwa akace dole toh ta fasa tafiyar, duk yadda Fauwaz da yazo yaso ya fahimtar da ita sam taki fahimta, kamar ma a tsorace take da al'amarin, gashi a wannan yanayi na insecurity babu yadda za'a yi a barta ta shiga mota, haka kuma a barta ita kadai ma matsala ce. "Yaya menene?" Tace tana matsawa kusa da ita "Yawwa gwara da Allah ya kawo ki, kiji dan wulakanci wai jirgi zamu hau idan zamu tafi." "Eh Yaya, ba bata lokaci nan da nan zaki ga anje." "Aikuwa banga uban da ya isa ya sakani hawa jirgi ba wallahi." "Har Baba?" Fauwaz yace yana dariya "Ko Kaka ne, ehe." "Ah abun azimun ne, bari na kira Baban da kansa yayi miki magana, kila shi yayi convincing dinki." "Duk ma me zakayi kayi, na gama magana." "Muje ki zauna Yaya, ki daina yawan fada kina tada hankalin ki dan Allah." "Toh yaran nan ne duk hanyar da zasu birkita min lissafi sun santa, ina dalili za'a ce dole sai na hau jirgi? Ai ba dole bace Habujan ko? A kyale ni dan Allah.". Sai ta fara tari da karfi, saurin tallafa mata jiddah tayi, ta mika mata ruwa tasha tarin ya lafa, zata cigaba da sababi Jidda tayi saurin cewa "Kiyi shiru karki sake tarin, ba in da zaki a jirgi, a mota zamu tafi ni dake sai su suyi ta hawa jirgin su." "Yawwa toh idan hakan ne na amince." Kallon Jidda Fauwaz yayi, kallon kunfi kusa ya juya yana ayyana yadda zai yiwa taurin kan Yayan. Be kira Baban ba kamar yadda yace, sai kawai yaje ya samo maganin bacci, ya ajiye a daki, da safe bayan sun shirya tsaf, sun fito ya dauko lemon exotic madaidaci ya saka mata maganin baccin dan daidai wanda ba zai bugar da ita ba, ya shiga part din ya sameta ta saka sabuwar atamfar ta, da sabon Hijabin ta fari kal, sai takalmin shima sabo tana cike da jin dadi ga sabon lalle a kafar yayi har ya soma duhu-duhu. "Ya ka gani?" "Kin fita fes fes ko ba sabula mutuniyar." "Godiya nake kaji, kasan fa kakanku tsabar dunkum dinsa ko yaba abu bayayi, ni bansan dadin kayi abu miji ya yaba ba, sai bakin rai da turbune fuska kamar shi aka dorawa baki daya matsalar Nigeria." "Innalillahi, wai Yaya ba zaki kyale bawan Allahn nan ya huta ba, ko me yayi ai yaci ace an yafe masa haka nan." "Toh ubana, sai ka fada min abinda ya kamata nayi tunda kai ka haife ni, ko kai kake bani ci da sha." "Allah ya huci zuciyar Hajiye Dije, ga exotic na kawo miki kisha idan kun shiga mota, sai mun hadu a chan dan mu dai jirgi zamu hau." "Ah ka kyauta, kasan kuwa dama na kwana biyu ban sha ba, shegen likitan nan bakin mugu wai a hanani shan kayan zaki kamar shine ubana, shikenan Alhaji yasa akai daina siyo min." "Yanzu dai gashi nan na kawo miki, kisha karki bawa kowa fa, naki ne ke kadai tawan." "Uban yan dadin baki, naji ni kira min jiddah mu dau hanya, kar muyi dare duk da dai ance sannu sannu bata hana zuwa sai dai a dade ba'a je." "Gani ma Yaya." Ta shigo sanye da atamfa lemon green and orange tayi mata kyau sosai har sa da Yaya ta kasa dauke ido daga kallon ta "Wai wai wai, chanchadi." A kunyace ta karaso ciki, Fauwaz yayi mata signal da ido yana nuna mata juice din hannun, ya fita. Bata gane komai ba, sai ga message dinsa bayan ya fita "Make sure tasha juice din nan, sai mun hadu a airport." Kallon juice din tayi ta kalli Yayan, "Kisha lemon naki Yaya sai mu tafi, an gama saka kayan a mota." "Auw toh." Tace tana bud'e murfin, ta kwankwade shi tas da dan sanyin sa dama, jidda ta karbi kwalin ta jefa a dustin sannan suka fito harabar gidan, ta taimaka mata ta shiga motar itama ta shiga, sannan suka fita daga gidan, suna fita motar su aunty itama ta bi bayan su ita da Usman sai Fauwaz din a gaba. Bacci ne ya soma daukar Yaya sama-sama, jiddah na kallon ta, ta gyara mata ta jingina sosai bacci me nauyi ya dauketa. Suna isa airport din aka samo wheelchair aka dora ta, aka sakata a cikin jirgin suka lula sai Abuja. ***Sabuwar Rayuwa! Sabon Shafi*** Baki sake Jidda take kallon garin yadda ya tsaro, bata dai taba hasaso haka Abujan take ba, ta dai san tana da kyau amma bata kawo haka ba,sosai yayi mata kyau kwarai, ta kalli Aunty sukayi ma juna murmushi, har lokacin Yaya tana ta sharbar baccin ta. Unguwar da suka shiga ita ta sake rikita Jidda har ma da Aunty duk da tana boyewa, babbar unguwa ce da manya manyan gine-gine tsararru, cikin tsari gwanin sha'awa. Shiru babu motsin kowa ba zaka taba cewa akwai halittu da suke rayuwa a cikin wajen ba A kofar wani babban tangamemen gate suka tsaya, gate din ya bude da kansa suka kutsa kai cikin katafaren filin gidan, wanda yake dauke da motici manya daga chan gefe, sai shuke-shuke masu ban sha'awa. Wani matashi ne yazo bayan sun tsaya, ya bud'e musu kofar ya russuna ya gaida Auntyn sannan yace "Ga part din chan." Ya mika keys din, karba Jiddah tayi, Fauwaz ya zagayo ya leka Yaaya da take ta sharbar bacci, ya kalli aunty ya kwashe da dariya "Ya za'a yi da ita yanzu Aunty?" "Ai baka kyauta ba wallahi,." "Aunty bansan ya za'a mata ba wallahi, kinsan kafiyar Yaya." "Ni dai kar a samu matsala fa." "Babu in sha Allah, peaceful bacci fa take, kuje bari na kirawo masu aikin nan na bq su taimaka sai a kai ta part dinta." "Je ka kirasu dai ina nan, Jidda jeki ke da Usman gani nan." "Toh." Tace ta rike hannun sa suka nufi shashen da aka nuna musu,tun kafin ta karasa take admiring ginin bare kuma ciki. Wani security ne daga gate ya taso, ya dan russuna ya gaida Auntyn sannan yace ko akwai matsala, girgiza masa kai tayi tace babu, ya bata hakuri ta koma wajen aikin su, gwada tashin Yayan tayi ta dan tattabata sannan ta kira sunan ta, a hankali ta bud'e idon da kad'an kad'an har ta gama gaba daya,sai ta kalli motar da take ciki ta kalli Aunty "Kar dai har mun karaso ina ta bacci." "Eh Yaya, ai wai ashe tunda kuka dauko hanya kike bacci zuwan ku kenan, jidda tace kina mota kina bacci shine nace bari nazo na taimaka miki." "Wai gaskia nasha bacci, awa nawa kenan ina baccin?" Ta zuro kafarta waje ta sakko, sai taga kamar lokacin suka baro gida, kamar zatayi magana kuma sai ta fasa hango Fauwaz na nufo su da wasu mata kedaru su biyu, kana ganin su kaga karfafa. "Ah ashe ma ta tashi." Sai ya juya wajen su yace "This is the second Madam, greet her." "Good morning Ma'am." "Good morning." Tace a takaice "You can go." Ya ce suka juya zuwa in da suka fito, salati Yaya ta rafka tana tafa hannu "Yanzu tsabar lalacewar ta kai lalacewa har da arna a gidan nan, na shiga uku ni Hajara yau naga abinda yafi karfi na." "Kai Yaya, house help ne fa, kuma ba arna bane kawai dai basa jin hausa ne." "Toh dan tsabar iyayi a rasa irin ma'aikatan da za'a dauka sai wannan zandara-zandaran zawarawa? Wai na shiga uku na lalace." "Fito na rakaki bangaren ki, kin ga yadda aka miki kuwa, harda katuwar TV ta bango gas fridge dinki cike da kayan dadi, kuma Baba yace zaa dauko miki gwaggo kuyi zaman ku." "Da gaske?" Ta washe baki tana fitowa gaba daya, "Muje ki gani, Anty sai mun shigo." Yace yana rike hannun Yayan, ita kuma Aunty ta nufi part din da jiddah ta shiga, wanda yake da yar tazara tsakanin su da wani hadadden part da yake a tsakiyar gidan wanda aunty ta tabbatar na matar gidan ne. A tsaye ta samu su jidda suna karewa yar karamar daular tasu kallo, ita kanta Auntyn sai da ta jinina, yayi kyau sosai duk da ba wani katon gani bane, kayan su aka shigo musu dasu, sannan Auntyn ta lallaka dakunan ta nunawa jiddah nata ita ma ta shiga nata. Amira ce kawai ta rage a gidan duk sun tafi school itama bacci ta koma bayan tayi sallah tunda tasan zuwan su jiddan ba lokacin bane. Wajen sha daya ta tashi, tana sakkowa daga gado tayo waje, suka hadu da Mama a falo tana duba wayarta, da kallo tabi Amiran kamar ta fuzgo ta, ta dake ta haka takeji dan yadda take son jiddah ko ciki daya suka fito sai haka. Bata dai kulata ba har ta fice ta kuma san in da zata dan taga shigowar su gidan ta window, ta kuma ga duk abinda ya faru tsakanin su da Yaya duk da bata ji me suke cewa ba, sakin curtain din tayi kawai ta cigaba da abinda takeyi. Da sassarfa ta isa part din sannan tayi knocking, Jidda ta zo ta bud'e suka rungume juna cikin tsananin farin cikin ganin juna. Fitowa Aunty tayi da murnar ta, Amiran ta gaishe ta sannan suka kule dakin jiddah ta tayata hade kayan ta waje daya a cikin wardrobe suna yi suna labari, yawanci akan school din da zasu fara zuwa ne next week da kuma yanayin rayuwar garin da yadda zasuyi mingling da yaran manya, ita dai jiddah ta san matsayin ta, bata sa a ranta zatayi rayuwa irin ta su ba, saffa saffa dai kar ta zak'e, duk da haka tasan dole ne ko taki ko taso rayuwar ta sai ta sauya ta sake daukar ta zuwa wani bigire na daban. ***Dawowar su Abuja ya sauya abubuwa da dama daga rayuwar Jiddah, sati daya cif da zuwan su suka fara zuwa wata private university a abujan, course daya sukeyi sai ya zama kullum tare suke duk in da kaga daya zaka ga daya. Sai dai a wajen da Jiddan tasan zai iya shafar matsayin ta na matar aure, wanda ta rike hakan da matukar muhimmanci, bata kuma sakaci bare ta yi wani abu da ya sabawa Allah. Sau biyu taje gaida Mama a satin da suka zo amma da kyar take amsawa, tayi saurin barin wajen, haka Jiddan zata tashi jiki a sanyaye ta bar part din, na farko aunty ce tace taje ta gaishe ta lallai dan da, da yanzu ba daya bane, akan haka taje amma sai data gwammace bata je ba, haka dai ta daure ta sake zuwa a karan kanta bayan Amira tazo wajensu tayi mata korafin zuwa nasu part din, nan ma dai same abinda ya faru da farko shi ya sake faruwa. Duk abinda ya faru bata fadawa Aunty ba, boye mata kawai tayi a matsayin babu komai dan taga yadda Auntyn take tada hankalin ta akan maganar auren. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (25) 1 year later Bayan shekara daya ***Abubuwa masu yawan gaske sun faru a cikin shekara gudun nan, Jidda ta samu sauyi na ban mamaki, yanayin society din, da yanayin rayuwar school da mutanen da suke mingling ya taimaka kwarai wajen karuwar wayewar ta, ta goge sosai musamman da dama bata da duhun kai, mutum ce da take kokarin tafiya da yanayin da yazo mata na sauyi cikin nutsuwa da karantar rayuwa. Rayuwar Abuja ba kamar rayuwar Kano bace musamman da suke mingling da mutane mabanbanta masu gogewa da wayewar sanin rayuwa, duk da haka bata yi wasa da martaba da darjaar da alalh ya dora mata ba, a matsayin ta, na me aure, dan iyakar kokarin ta, tayi wajen kare kanta da duk wani abu da tainakon aunty da nasihar Baffa da baya kwana biyu sai ya tisa mata matsayin ta, da ita din wacece. Bata da matsala kowacce iri ce, duk wani abu na jin dadin rayuwar Baba yana musu musamman ma ita da ya dauke responsibility din Tariq, hatta abinda bata ce tana so ba yi mata yake yi, tsakanin ta da Mama babu shiru daga gaisuwa shikenan shima ba wai tana amsa mata kai tsaye bane. Hakan tun yana damunta har ta hakura ya daina damun ta, bayan Aunty ta zaunar da ita tayi mata bayanin dalilin daukar zafin Maman na rashin sanar da ita komai sai bayan an daura, wanda Aunty tayi mata uzuri sosai dan tabbas tasan baa kyauta mata ba, hakan yasa Jiddah cire damuwar yadda Maman take mata cike da fatan watarana zata so ta, ta karbe ta kamar yadda sauran iyayen miji ke karbar matan yayan su. Fitowar ta kenan daga wanka sun samu hutun end of semester saboda haka basa fita musamman ma ita dan su amira an samu kafar yawo ba'a zama kwata - kwata, tun wanchan satin labarin dawowar Ya Tariq ya sameta, sai taji gaba daya ta rasa nutsuwa da sukunin ta, duk abinda take tunanin yadda zata kaya take, duk da a kullum Ya Fauwaz da Amira na kara mata kwarin guiwar babu namijin da zai ki ta, a yadda take a yanzu, da haka ta samu dan peace of mind har take biyewa aunty da Yaya wajen shirya ta. Riga da skirt na cotton material ta dauko ta saka, sai taji skirt din ya matse ta, kusan dukka skirt dinta sun matse ta saboda yadda ta samu sauyi a jikin ta, a lokaci daya, duk da har yanzu bata da wata kiba ta azo a gani amma babu laifi tana da front and back shape dinta me matukar kyau da daukar hankali shiyasa a kullum take cikin shigar kirki haka idan Ya Fauwaz zai shigo takan saka madaidacin Hijab akan kayan ta, ita kanta mamakin kanta take da yadda a lokaci daya ta ciko ta bayan amma cikin ta kamar bata zuba masa komai saboda yadda yake flat a koda yaushe. Zare skirt din tayi da kyar ta dauko doguwar riga plain ta saka kawai ta yafa medium veil a kan dogon gashin ta wanda ta nannade shi ta tura shi a cikin gashin saboda yadda yake sakkowa gadon bayanta duk lokacin da ta sake shi. Part din Yaya ta nufa in da ake mata gyaran jiki, a chan ta samu su Amira dukkan su tare da me gyaran jikin. Bikin Safiyya da Umaima za'a yi, sai Baba yace sai a hada da na su Jidda din suma ayi shagalin bikin tare, sanda ya fada sai da fuskar Mama ta chanja sosai dan ko sunan Jidda bata so taji ana hadawa da na Tariq, dan dai ma ta shirya nuna musu itama nata karfin ikon akan Tariq din, shiyasa take bin komai a sannu kar ta bata goma biyar bata gyaru ba. Tare ake musu gyaran jikin da matar da maman ta dauko tayi musu dan shirin biki take gagarumi, kasancewar bata son abun magana shiyasa tace su zauna a wajen Yaya anayi musu dukka a chan dan bata son shige da fice a part dinta. Tana shiga Amira da Maryam suka hau tafi "Kinga yadda kike glowing matar yaya, lallai idan Ya Tariq ya dawo sai ya kusan susucewa akan ki, ji yadda fa fataarki ta zama kamar ta jarirai." Dariya ta saka, ta kai wa Amira dake kusa da ita dundu ta goce "Kun cika sharri wallahi." "Allah kuwa, dan Allah Aunty Yagana baki ga yadda skin dinta ya kara komawa ba?" "Na gani fa." "Toh kinji dai, ba wai zuga ki muke ba." "Yo idan ma zugar ce kuyi tayi mana, nan gani da nan bari dumamen mayya." Yaya ta shiga zancen tana hararar su "Kai Yaya, me yayi zafi har da bakar magana." "Anyi din, iyayi ne ni bana so." Tace tana yatsine fuska. Harara ta Maryam tayi tana juyar da fuskar ta gefen da babu kowa amma da Yayan take, shewa tayi ta buga zani, ta taso har gaban su tace "Bansan anayi ba, kunu a wani gida, idan an isa dai a yi a gabana mana." "Yaya dai kina son tarewa Jidda abinda mu fa wasa muke tsakanin mu, amma kin hakikance kamar gaske, haba!" "Cewa tayi tana son wasa ne, kaji min yara, ba matar yayanku bace, ku bata girmanta" "Kai innalillahi, wallahi Yaya zama dake sai an shirya, duk dai take-taken korar mu kike daga wajen nan, ba kuma in da zamu wallahi." "Sai kuyi tayi ai, jaraba. Taso Jidda muje kiga wani abu, irin hade-haden tsofaffi ne amma yafi shirmen da ake baku na wannan zamanin." "Ahaap, dama duk munsan kwanan zancen, shiyasa kike korarmu, wallahi Jidda ki kiyayi concoction din da Yaya take hada miki, sai kinje ta zugar miki da ciki kafin karshen sati kizo duk ki rame." Maryam tace tana yin hanyar fita dan tasan ko ta zauna ma Yaya sai ta mata dundu "Ba ruwanku, tsakanin mu ne da Yayata." Jidda tace tana dariya, "Shikenan mu yan kallo ne." "Muje Yaya ki bani." Taja hannun Yaya, suka shige bedroom dinta, ta karbi hadin a wata robar ruwan nestle, ta ce zata je tasha a daki, da wayo dai ta lallaba yayan ta raba ta dashi, sannan taje ta ajiye a kitchen din part din Aunty ta dawo aka shiga yi mata gyaran jikin. ***Mama na zaune suna waya da Aunty Nafi tana sake kasheda mata kar ta kuskura yarda da zabin da akayi ma Tariq gwara ko Salma ce su hada su. Shiru Mama tayi tana jin ta, duk da dai bata son jiddah amma ba zata yi wa Tariq irin auren da Baba yayi masa ba, zata bashi damar ya kawo wadda yake so da kansa tunda ba wai ta gamsu da tarbiyyar Salman bane duk kuwa da alakar su. Sallama sukayi ta katse kiran ta kira Tariq din da Ishaq ya jashi zuwa yin siyayyar abubuwan da zasu taho dasu gida, da fari ki yayi amma da yayi convincing dinsa sai ya yarda ya bishi. kayayyaki ya sissiyo nasa sai kuma ya siya ma yan gidan nasu kaf har Aunty da Usman. Suna hanyar dawowa kiran Maman ya shigo, ya daga yana gyara Bluetooth din dake kunnen sa "Tariq." Ta kira sunan cikin yanayin nuna kaguwa "Mama barka da gida, kuna lafiya?" "Alhamdulillah, ya shirye-shiryen tahowa?" "Gashi fa, muna yi yanzu muke komawa gida daga shopping " "Masha Allah, we all can't wait to see you " "Nima Mama." "Um um kai ai baka damu ka ganmu ba, tunda kiri-kiri kaki zuwar mana ko hutu ne, nima kuma ka hanani zuwa." "Toh gashi Mama yanzu har an gama zan dawo ma." "Still dai." "Toh I'm sorry, ba zan sake ba." Murmushi tayi me sauti ganin yadda Tariq din yake waya da ita, tabbas akwai sauyi sosai a dangane da mu'amular sa, yanzu kuma an kara girma dole abubuwa zasu chanja "Shikenan toh, sai kun isa gida ka kirani akwai sakon kayan da nake so kaje ka siya ma sisters din ka." "Ok Ma, ina komawa zan kira." "Allah yayi maka albarka." "Amin." Ya amsa cike da jin dadin addu'ar da tafi masa kowacce. ***Sati biyu ya rage bikin gidan duk shirye-shiryen da ya kamata ayi duk an yi hatta wajen da za'a yi shagalin an kama komai dai cikin tsari dan ba karamin shiri akayi ba. Duk da kudurin Mama na ganin Tariq ya ki Jidda hakan be hana ta cigaba da duk shirye-shiryen tare da jiddan ba, hakan ma cikin kissar tace dan bata son ta sake nunawa Baba itace bata so, tafi so Tariq din yazo da kansa wanda tasan tilas ne yaki jidda. Su uku ne a motar, Ya Fauwaz da yake tukawa, Umaima na gaba sai ita da Ya Safiyya a baya, hira suke gwanin sha'awa dan ita babu abinda zata ce tsakanin ta dasu sai godiya musamman tun bayan da aka daura auren ta da Tariq suka sake jan ta a jiki sosai. A gajiye suke dan duk abinda suka san zasu bukata sun siya dan ba kuma sake fita zasuyi ba inji Mama, ita dai Aunty tana gefe tana kallon ikon Allah dan dai duk wani abu da ya kamata ayi wa Jiddan Mama da Yaya sun dauke, sai dan abinda ba za'a rasa ba. Kayan ta ta dauka a booth, Ya Fauwaz yayi saurin karbewa yana girgiza mata kai "So kike Ya Tariq ya dawo ya hukunta ni kenan, na bar her royal highness da daukar kaya." "Gaskia dai Ya Fauwaz." Umaima tace tana dariya "Muje na kai miki dan nasan idan ya dawo gobe duk sai ya bincike mu yadda mukayi treating dinki idan ya samu daddad'an labarin nan." "Ya Fauwaz kai ko?" "Ai gaskiya ce." Safiyya tace suka saka dariya. Tare suka jera dashi yana sake tabbatar mata da yakinin sa na yadda zata sace zuciyar Ya Tariq a lokaci daya, duk da akwai tsoro sosai a k'asan zuciyar ta amma duk sanda Ya Fauwaz ya bata hope sai taji tana samun kwarin guiwa, sau tari ta kan hau kan profile dinsa tana duba shi, ta kan ganshi online wani lokaci duk da ba kasafai ya cika hawa ba, tasha gwada yi masa magana sai ta kasa, tayi hakuri sosai sai gashi har lokacin yazo. Ajiye mata kayan yayi a falon Antyn, ya juya yana sake jaddada mata gobe ne fa, murmushi kawai tayi ta tattare kayan ta wuce dakin ta, ta ajiye su ta shiga toilet don yin alwala. ***Washegari da wuri kowa ya tashi a gidan, cikin shirye-shiryen tarbar shi, Mama ta kasa zaune ta kasa tsaye da gaske take cike da farin cikin dawowar sa, har ta gaza boyewa, sai da Baba ya tsokane ta. Bangaren Hajiya Yaya ma tana cike da farin cikin dawowar sa, wanda ko ba'a fada ba a cikin jikokin nata tafi son Tariq din, saidai yanayin sa tasa suke rigima sosai har ka zata ko bata yin shi ne. Tsaye take a kitchen ita da Aunty suna shirya masa girki, mai rai da lafiya, baki daya ta bada dukkan attention dinta akan girkin, duk da sun fara da wuri amma har aka zo tafiya airport dauko shi bata gama ma bare ta samu tayi wanka, Amira ce ta leko kitchen din da ganta da doguwar riga zurum tana ta aiki ta kwashe da dariya "An shirya fa, har ma mun fito nace bari na leko ki." "Ai dama ba zuwa zan ba Amira, sauri dai nake naje nayi wanka." "Auw har Ya Fauwaz yace ki fito." "A ah kuje, sai kun dawo." "Ok matar Yaya." Dariya sukayi a tare ta fice ita kuma ta maida hankalin ta akan aikin, ganin lokaci na tafiya ya saka aunty cewa taje tayi wanka zata karasa ita da Badiya me aikin ta. Wanke hannun ta tayi a sink ta fice da sauri ta fada toilet. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (27) ***Chan wajen gate ya nufa, fuskar sa a hade,ya tambayi ina driver, ya taso da sauri ya bud'e masa motar ya shiga, ya tada motar suka fice daga gidan. Jingina kansa yayi a jikin kujerar ya saka hannu zai ciro wayarsa ya tuno ya barta a daki sanda Fauwaz yake masa magana, tsaki yaja kawai ya maida kansa da yake sara masa, daga dawowar sa sai a nemi a hanashi sukuni haka kawai, ya rasa me yasa Yaya take son kure shi, idan ba haka ba har shine za'a yiwa aure irin wannan? Shi da ko tunanin rayuwar auren ma baya yi yanzu yake son settling ya fara neman yarinyar ma.   Yasmin ce ta fado masa, ya tuna sanda ta rike masa suitcase tana hawaye, wai a dole bata so ya tafi, shi dariya ma ta bashi yadda ta hakikance ita tsakani da Allah take son shi, bayan yasan irin wannan soyayyar bata existing sam. Shi be ma yadda da irin wannan ba, kamar wani wason kwaikwayo haka ya dauki abun, yawo sukayi tayi akan street din Abujan daga wannan su sauka wannan sai da ya gaji kuma ya tuna Baba zai iya dawowa ya nemi shi sannan yace su koma gida.    Baba na harabar gidan tare da wasu mutane suka shigo, zuciyar sa ce yaji ta dan ragu da zafin da take masa ganin Baba, kallon motar Baban yake har suka samu waje sukayi parking ya fito da saurin sa, ya nufi wajen su. Fuskar Baban ce ta fadada da fara'a ganin Tariq din. "Tariq..." "Baba barka da warhaka." Ya russuna k'asa yace "Ina wuni?" "Lafiya lou bakon turai." "Ina wuni?"    Ya gaishe da wadanda suke tare da Baban, suka amsa sai sukayi masa sallama suka tafi. Hannun sa Baba ya kama ya rike suka shiga takawa zuwa part din Yaya suna tafiya yana tambayar shi hanya da sauran abubuwan da ya kamata ya tambaya.    Tare suka shiga Tariq kamar ya kwace ya gudu dan baya son abinda zai hada shi da Yaya a wannan lokacin, so yake ma yaje yayi tunani sosai akan maganar da Fauwaz yayi masa. Hannun sa da yake cikin na Baban ya kalla kamar ya kwace ya daure dai suka shiga falon. Tana kwance tana gyangyad'i suka shigo tayi firgigit ta tashi pretending kamar ba bacci take ba "Yaya bacci kike ne?" Baba ya tambaya "Um um, ba bacci nake ba, kallo ma nake abina." _"Musun me bacci."_ Tariq yace a k'asan makoshin sa "Dunkum sabon ango ashe tare kuke." Gimtse fuska yayi, Baba kuma yayi dariya ya zauna ya gaida Yayan sannan Tariq ma ya gaishe ta da k'yar. "Wai Yaya ya akayi ne ranar baki bani labarin jirgi ba, ya kika ji?" "Jirgi ni Hajara, ai ban hau ba, su dai chan suka hau ni da Jidda muka bi hanya nan da nan muka isa mu ma." "Baki hau jirgi ba Yaya? A ah ko dai bacci kikayi dai bayan kun shiga?" "Da ido na biyu sarai ni banga an hau jirgi ba." "Ah toh inaga hakan ne, toh shikenan." "Yawwa." Tace tana gyara daurin kallabin ta "Dama kawo miki shi nayi Yaya, gashi nan tunda Allah yayi ya dawo, sai a sanar dashi abinda yake faruwa ba sai an wani jira ko bata lokaci ba." "Tabbas, tunda dai yarinyar nan dai tayi hakuri zaman jiran shekara guda ai ba wasa bane." "Tariq..." Baba ya kira sunan sa, gaban sa ne ya fadi, ya daure da k'yar ya amsa "Na'am Baba." "Masha Allah, toh magana ce guda daya zuwa biyu, na farko dai mun yi maka wani abun alkhairi duk da babu sanin ka, amma sanin cewa Tariq ba me bijire umarnin iyaye da magabatan sa bane, nasan ba zai taba wasa mana k'asa a ido ba, shiyasa har mukayi maka abinda mu muke ganin gata ne, muka aura maka kanwar ka Hauwa'u." Shiru yayi kamar ruwa ya chinye shi, adam apple dinsa ya dinga motsawa yana yin sama da k'asa, haka yake a duk lokacin da ransa ya baci. Duk a tunani da halokokon sa ai auren ake shirin hadawa, kenan har an daura tsawon shekara daya kenan idan har kunnen sa ya ji masa daidai. "Yarinya me hankali da nutsuwa, sam bata bijire mana ko kin bin umarnin mu ba, cikin saukin kai ta amsa mana." Yaya ta dora tana kallon Tariq din da yayi tsam yana jin kamar an sassare masa kafafunsa. "Muna fatan zakayi mana biyayya kamar yadda Hauwa'u tayi mana, in sha Allahu ba zakayi dana sanin karbar zabin mu ba." "Nagode Baba, Allah ya kara girma." Yace yana damke hannun sa. Fuskar Baban ce ta fadada da fara'a, ya shiga sakawa Tariq din albarka, Yaya tana amsawa. Da k'yar ya mike ya fito daga part din, yana fitowa yasa dukkan karfin sa ya bigi ginin wajen "Damn it!" Ya fada yana yarfe hannu, gaba yayi kamar zai koma part din Mama, sai kuma ya dawo ya wuce gate ya zauna a wata kujera yana jin dama be dawo ba, yana zaune yaga fitowar Baba daga part din Yaya, sai ya tashi da sauri ya nufi part din ya shiga yana kumbura ya sameta ta cire riga sai daurin kirji alamun kwanciya zatayi "Ya akayi?" Tace ganin ya tsaya daga kofa yana cika yana batsewa "Bana son yarinyar nan, gwara ma a raba auren nan dan ba zan taba iya zaman aure da ita ba." "Na'am? Kace me?" "Bana son ta, bana son auren." Matsowa kofar Yaya tayi tana kallon fuskar sa "Ina jinka, baka so kace ko?" "Eh, dan Allah Yaya, ki taimaka min." "Tam, zan taimaka maka, amma ka bani sati uku ayi shagalin bikin nan a gama, ni nasan yadda zan bullowa al'amarin dan nima ba wai inason auren naku bane, tunda kuma kace baka so ai an gama." Kallon ta yayi a cikin ido, ta gid'a masa kai alamar eh, ta gimtse fuska kamar gaske, "Shikenan tom, dan Allah kiyi yadda zakiyi." "Dole na, yanzu dai ka kwantar da hankalin kar Babanku yace baka masa biyayya ba, ka barmun komai a hannu na, Kaje yanzu ka huta ka kwanta." "Nagode Yaya, nagode sosai." "Karka damu yiwa kaine." Tace tana dariya Fita yayi ta bishi da harara sannan ta rufo kofar ta "Ja'iri zaka yi bayani ne, idan ma aljanun suka zugo ka daidai nake da su wallahi." Yana fita yaji zuciyar sa ta dan yi sanyi, maimakon ya wuce bangaren su sai ya juya zuwa part din Auntyn dan yana so yaje yaga yarinyar da tsaurin idonta har ya kai ta yarda a hada su aure, sai ya nuna mata iyakar ta, da matsayinta dan shi ba sa'an ta bane, tukunna ma nawa yarinyar take? Dole ya koya mata hankalin da zata je ta samu Baba da kanta tace ta fasa. Knocking yayi a kofar da dan karfi, shiru ya sake kwankwasawa sai ya gwada turawa, ta bud'e ya shiga yana kallon falon da yake a share neat sai kamshin turaren wuta da yake tashi me sanyin kamshi, shak'ar turaren yayi ya kalli katotuwar television din dake tayi ita an kunna cartoon network. Aunty na part din Baba dan yau itace da gidan, shiyasa shirun yayi yawa masu aikin kuma duk sun wuce bq, tunawa da yayi da babu abinda yasa a cikin sa yasa shi tunawa da abincin da yaji kamshin sa dazu. Tana tsaye a kitchen sanye da doguwar sakakkiyar rigar bacci me dan kauri, kanta babu ko dan kwali tana tsaye gaban microwave tana warming abincin da akayi dazun don shi wanda Fauwaz ne kawai yaci sai Aunty da masu aikin. Tun da ta dawo daga wajen su dazun aunty tace a kai masa sai ta doje tace baya nan sun fita, har magriba Aunty ta sake tambayar Fauwaz yace eh ya dan fita be dawo ba, har ta gaji tace a saka a fridge kawai ta tafi part din Baban. Yunwa ce yanzu ma ta taso ta, bayan ta shaki kukan ta, ta koshi ta gode Allah, taji ciwo fiye da tunanin me tunani, amma ba zata taba bari ko Amira taga weakness dinta ba, dazu ma haka Fauwaz ya sake kiranta amma ta nuna masa babu komai, duk da deep down she's hurt, very hurt da ta kasa iya daukar abun, da kunnenta taji yana ikirarin ba zai so ta ba, tayi masa siranta da yawa, ba ajin sa bace. tabbas duk abinda ya fada haka ne, amma kuma zuciyar ta, ta k'asa karbar gaskiyaar yafi karfin nata, shiyasa har abun ya tsaya mata a ranta sosai. Kashe microwave din tayi, ta dora abincin akan dan madaidacin tray ta saka ruwa da lemon kwakwar da duk shi akayi wa. Zuciyar ta ce ta sake karyewa tana kokarin daukar abincin, sai ta dora kanta akan kitchen cabinet din ta sake sakin kuka me cin rai. Kitchen din ya nufo, da niyyar ya duba abincin ko zai samu, sai yaji kamar shasshekar kuka k'asa -kasa, da dan saurin sa ya karasa kofar, ya hangi bayan ta, kanta a duk'e tana fidda sautin kuka irin me taba ran duk me saurare. Gashin kanta idanun sa suka sauka akai, ya bud'e baki cike da mamakin tsawo da bakin sa, yana tsaye ta ware hannun ta, ta jawo tissue dake gefen daman ta, ya bi dogayen zarara-zararan hannayen nata da kallo, sun sha kunshi baki da ja me matukar kyau da daukar hankali abinka da farar mace. Yana nan a tsaye ta gama share fuskar ta, ta jefa tissue din a dustbin ta daga kanta sama tana kokarin maida ragowar kukan da yake taso mata, sannan ta sauke ta dauki tray din a hannun ta, ta juyo idanun ta suka shiga cikin nasa, yana tsaye a jingina da jikin kofar yana kallon ta, irin kallon wacece ke? Irin kallon da ya fara yi mata ranar da ya fara ganin ta. Duk da ya chanja yayi kiba da haske fatar sa ta murje, amma be sauya mata ba, shi din ne dai na ranar farkon nan, idanun sa a shanye kamar me jin bacci, kallo daya biyu tayi masa, sai kalaman sa suka shiga dawowa mata daya bayan daya, da sauri ta sauke kanta k'asa zuciyar ta na harbawa, da sauri da sauri, daga kafar ta, tayi daga wajen da take tsaye, tazo ta gifta ta gefen sa, har jikin ta na gogar nasa dan yadda ya cinye kusan fiye da rabin kofar. Juyowa yayi ya bita da kallo, har ta shige dan corridor din da zai kaita dakin ta, tana shiga tayi saurin dire tray din ta saka key a kofar, ta durkusa a wajen tana sakin kuka. _INA MASOYA KUMA MA'ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._ _TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_ _A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_ _SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_ _AKWAI TURAREN *AL'AJABU NA TSUGUNNO DA KHUMRAH* DIN SA_ _SANNAN SU NA DA *TURAREN GASHI NA CREAM DA KUMA SPRAY DIN SA NA FESAWA*_ _BA ANAN SUKA TSAYA BA. SU NA DA *TURAREN MOPPING, DA NA BANDAKI AKWAI NA RUWAN WANKI DA NA FESAWA A DRAWER KO AKWATI*_ _AKWAI KAYAN GYARARRAKI NA FATA. KUJERAR TSUGUNNO, KASAKE NA WUTA, COAL IGNITER TA KUNNA GARWASHI, ELECTRIC BURNERS DA ENGLISH COAL_ _AKWAI LAFFAYAS DA SAURAN TURARUKA NA KAMSHI KALA KALA_ _SU NA BADA KAYAYYAKIN SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYA AKAN DAYA DAYA. SANNAN SUNA TURA KAYAYYAKIN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE. KAYAN SU YAN CHADI NE DA SUDAN DA KUMA YERWA WATO MAIDUGURI._ _KYAU, INGANCI DA RAHUSA SAI KAYAYYAKIN KAMFAMIN YERWA INCENSE AND MORE. SAI KUN GWADA ZAKU BAMU LABARI_ _NAMBAR TARHON SU DA ZAA KIRA KO MUSU MAGANA TA WHATSAPP ITACE: 08095215215_ _INSTAGRAM HANDLE DIN SU: @yerwaincense_and_more_ _YERWA INCENSE AND MORE: A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS AND MORE_ [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (26) Tana tsaye a gaban mirror taji shigowar motocin alamun sun dawo, gaban ta ne ya fadi cikin ta yayi wata irin murdawa, ji tayi kamar tana bukatar shiga toilet amma tasan irin wannan yanayin ne da mutum yake tsintar kansa when he's nervous. Tafin hannun ta ne taji yana mata wani iri sai kuma tafi kafarta, samun waje tayi ta zauna da sauri tana sauke tagwayen ajiyar zuciya, ta dan dan mintuna a haka kafin ta tashi ta karasa shiryawa cikin sabon kayan ta riga da skirt, ta yafa madaidacin chantilly akan kayan nata, ta feshe jikin ta da turare me sanyin kamshi, wanda baya hawa ka. ***Kafafunsa ya zuro sanda suka iso cikin gidan nasu, idanun sa na kan gidan da yanayin tsarin gine-gine wanda yayi saurin banbance kowanne,. "Ina wajen Mama?" Yace bayan ya fito daga motar, da hannu Fauwaz ya nuna masa, yana kokarin bawa yaran dake harabar gidan masu kula da gyaran compound din da duk aiken gidan jakunkunan Tariq din dan kai mishi su part dinsu. Takawa ya shiga yi zuwa part din Maman wanda tuni su Maryam sun isar mata da labarin isowar sa, tana tsaye a tsakiyar falon ya turo kofar ya shigo, ta saki baki ganin wani irin chanjawa da Tariq din yayi. Murmushi ya sakar mata yana karasa ciki da dan saurin sa, ya russuna ya gaida Maman bata san lokacin da ta rungume shi ba. "Welcome home son, sannu da hanya." Ta sake shi tana fada, sai kuma tace ya zauna, ya zauna bayan ya dan kalli falon. Gaishe ta ya sakeyi sannan sukayi maganar bayan rabuwa, ta saka aka kawo masa ruwa da juice yasha ruwan kawai tace sauran abincin suna chan a part dinsu aka jera masa, mikewa yayi yana zuwa hannun sa a cikin dogon wandon sa yace zai je ya huta zai shigo anjima. Har kofa ta raka shi cike da jin dadin ganin sa. Yana fita suka hadu da Fauwaz ya gama shigar masa da kayan, ratayo kafadar sa yayi ya yi maganar a hankali "Rakani na gaida Aunty, sai Yaya daga nan ina so na huta dan wani banzan transit mukayi a Ethiopia wanda yayi draining baki daya energy dina." "Wai, matsalar kenan dama, ina zamu fara zuwa?" "Wajen aunty, dan Yaya idan naje surutun ta nasan zai kara min ciwon kai, kaga ina fitowa sai naje na huta gaba daya." "Allah ya dawo damu ai, kai da Yaya ai kamar Tom and Jerry, Jidda ce kawai daidai da ita ta iya lallaba ta wallahi." "Jidda?" Ya kira sunan kamar me tunani, sai kuma yace "Ohh, that slim girl?" Dariya ya bawa Fauwaz,be bashi amsa ba saboda karasowa part din Auntyn da sukayi, suka shiga Fauwaz na gaba yana bin sa a baya yana nazarin part din shima, kamshin abinci ne ya daki hancin sa, irin kamshin da be taba jin irin sa ba, lumshe idon sa yayi ya bude sanda Auntyn ta fito fuskar ta cike da fara'a tana masa maraba, murmushi yayi ya amsa sannan suka dan taba hira, yace zai dawo ya mike sai kuma ya tsaya "Aunty wannan kamshin abincin, inason naci" "Naka ne ai, tunda dan kai Jidda tayi." Shiru yayi kamar ruwa ya cinye shi, sai kuma ya kada kansa alamun ok, sannan yace "Zamu ci dadi." "Sosai, jiddah expect ce in dai girki ne." Ya Fauwaz ya kara dan duk ya sake samun hanyar convincing dinsa. Gid'a kansa yayi, yace suje suka fita sai part din Yaya, wadda ta cika tayi fam dan tunda tasan sun shigo take zurara ido a hanya amma dan wulakanci sai yaje ya gaida uwarsa sannn zai zo wajen ta. Suna shigowa ta tsuke fuska kamar ba jiran shi take ba, kallon fuskar ta yayi sai ta bashi dariya ganin yadda tayi kicin kicin da fuska ita a dole tayi fushi, fushin da be san na menene ba. "Ai da ma baka zo ba, tunda sai ka gama gaida iyayen ka zaka zo waje na." "This woman and her wahala." Yayi maganar a kasan makoshin sa, ya zauna a gefen kafarta yace "Yi hakuri bazan kara ba." "Dama ba laifi kayi ba..." Tace kunya kuma sai ta kama ta yadda tayi masa bayan dawowar sa kenan "Mun same ku lafiya?" "Alhamdulillah, Allah ya kaddara saduwar mu, na zata fa da sai mun mutu zaka zo taaziyya." "A ah, ban isa ba." Yace yana murmushi "Ikon Allah, ashe dama kana murmushi, dama dan uwanka yana murmushi kai." Ta kalli Fauwaz tana rike haba "Dariya ma har da kyalkyalawa." "Ah lallai magani yayi aiki, dole na kira Malam na sake godiya, ya kuma sake aiko maka da wani rubutun." "Ai naji dadin maganin nan Yaya, nagode sosai." Yace yana biye mata dan ya gano da dadewa wahalar da kansa kawai yayi da ya kasa fuskantar halin Yayan "Ba komai ai yiwa kai ne, ka dai samu daddad'an labarin bikin ka wajen ita uwar taku ko?" "Biki? Wanne biki Yaya?" "Bari Yaya zan masa bayani kinji?" "Wanne biki ake magana Fauwaz?" "Muje part din mu, muyi magana." "Ok." Yace a sanyaye, ya tashi suka fita, ita dai Yaya ko a jikinta, murnar ta kawai take tasan kuma duk tsiyar Tariq din ba zai taba kin jiddaa ba. Suna shiga part din nasu Fauwaz yayi wa Jidda text wadda take rufe a daki tun shigowar su wajen Auntyn har suka fita, tana jiyo echo din muryoyin su amma ta kasa fitowa "Kawo ruwa part dinmu jiddah." Ta karanta text din, sai ta mike tana sake kallon kanta a mudubi, kafin ta fito ta shiga kitchen ta dora ruwa akan tray tare da cup ta fita zuwa part din su Fauwaz din. Ransa ne yayi kololowar tun kafin ma Fauwaz ya gama maganar, ya dakatar dashi ba tare da ya gama fahimtar abinda ma yake nufi ba, abu daya kawai ya tsaya ya fuskanta shine ana so a hada shi aure da figaggiiyar yarinyar nan jidda, be ma ji karshen bayanin ba, bare yaji har ma an daura musu auren shekara daya kenan. Hannu yasa ya dakatar da Fauwaz din ta hanyar cewa "Ya isa!!!" “Ya Tariq amma…” Fauwaz yace zai cigaba da bayanin “Look fauwaz, ba zan iya auran yarinyar nan ba, tayi min kankanta da yawa, plus bata cikin spec dina gaskiya. Bana so mace ta cika siranta da yawa, plus she’s young. Very very young da rainon ta zanji ko da aiki na!?” “I know, amma when last kaga Jidda? When last ka ganta face-to-face?” “Ba zan iya tunawa ba, infact na manta kamar ta ma baki daya ni. So it’s better kaje ka sanar da Yayah, ba zan iya ba gaskiya, gobe goben nan zan koma in da na fito, daga dawowata? Haba!” “Calm down and give it a second thought, karka yanke shawara base on abinda ka sani a baya, jiddan da ka sani shekara biyar baya ba itace wannan Jiddan ba! Ka daure ka ganta.” “Fauwaz!” Sai ya mike tsaye “Kana bata bakin kane kawai, ba zan iya ba gaskiya, ba zan daukar ma kaina abinda na san ba zan taba iyawa ba.” Mikewa shima yayi, yana girgiza masa kai, zai yi magana ya daga masa hannu “Bana son sake jin komai. Ya isa haka nan, ba zan taba iya soyayya da ita ba, bare har ta kai ga maganar aure! Never!!! ****Tray din ruwan da yake hannun ta ne yake neman subucewa, tayi saurin rike shi hawaye na saukowa a kuncin ta, ya zatayi da auren sa da yake kanta? Ya zatayi da rayuwar ta yanzu kenan? Innalillah wa inna ilaihi raji’un. Ta shiga maimaitawa. Takun takalmin sa ne ya iske ta, tayi saurin matsawa jikin dan corridor din dake jikin dakin ta makale, fuskar sa a hade take tsaf, yana cikin shigar farar tshirt wuyan sa sakale da necktie navy blue sai dogon wandon chinos dake sanya a jikin sa. Dogo ne sambal, kuma giant na ajin karshe, zuwa yayi ya wuce ta, ba tare da ya lura da ita ba, tana jin kiran da Ya Fauwaz yake kwala masa amma yayi biris kamar be ji ba. Ya wuce kansa a gaba cikin yanayin da ta kasa hange ko hasashen sa. Ji tayi tamkar kafarta ba zata iya daukar ta ba, duniyar na juya mata, shekara guda kenan tana dauke da igiyar auren sa, igiyar da ta raba ta isma’il me tsananin son ta da kaunar ta, ta zabi zaman dakon jiran shi, duk da bata da yakinin abinda zata tarar daga gareshi. Zuciyarta tayi nisa a kaunar sa wanda har take jin bata da wani katabus idan har babu shi. Me yasa zuciyar ta, ta zalunce ta? Me yasa ta sakata kaunar wanda baya son ko ganin ta? Lallai zuciyar ta, ta zalunce ta zalunce mafi girma. Zaman dirshan tayi a wajen, cup din da ruwan kowanne yayi nasa wajen, Fauwaz ne ya fito, ya ganta a wajen, yanayin da take ciki ya tabbatar masa da lallai taji maganganun su, durkusawa yayi a gabanta cikin yanayin tausayinta, dan yasan yadda take son Ya Tariq, kuma yasan sune ummul abaisin gina mata soyayyar shi a cikin zuciyar ta, shi da Amira sune suka bata hope, suka dora ta akan turbar da a yanzu shi kansa be san da wanne irin baki zaiyi amfani wajen gyara matsalar ba. “Jiddah.” Ya kira sunan ta cikin yanayin da shi kansa yasan abinda zai fada bashi da wata maana, dago manyan dara-daran idanun ta tayi, wanda a kullum suke cike da wani haske me kyawun gaske, sai dai a yanzu sun rine sun koma wasu iri na daban, tamkar ba su. “Nasan kinji komai da muka ce, bansan me kuma zan ce miki da zai karfafa miki guiwa ba, amma na miki alkawari sai Ya Tariq ya kawo kansa wajenki, begging you on his two knees akan ki taimaka masa. Nayi miki wannan alkawarin, sai ya sauke duk wata izza da yake ji, sai ya ajiye duk wani self respect nasa, ya nemi soyayyar ki.” Girgiza masa kai tayi, ta mike tana karkade jikinta, ya taimaka mata ya dauki tray din yana leka fuskar ta da ya kasa gane ainihin abinda yake faruwa a cikin zuciyar ta “I’m so sorry Jidda.” Murmurshi ta sakar masa wanda yake dauke da abubuwa masu yawan gaske, ta shiga takawa zuwa cikin gidan, gefen ta ya tsaya suke jera yana rike da tray din, suka shiga cikin gidan zuwa part din antyn, a saman madaidacin fridge din dake falon ya ajiye tray din ita kuma tayi saurin shigewa dakin ta, tana shiga ta kulle kofar ta jingina da bayan kofar zuciyar ta na bugawa da karfi da karfi “Ina son ki Jiddah, ina son ki fiye da yadda nake son kai na, dan Allah ki ceci rayuwata ki so ni ko da kwatan son da nake miki ne.” “Kayi hakuri isma’il, ba zan iya ba, ba zan iya ba.” “Shikenan Jidda, shikenan sai watarana!” Kalaman Isma’il na karshe kenan, anya ba alhakin sa bane zai fara bibiyarta? Anya? Ashe haka kake ji idan wanda kake so ya furta maka kalmar baya son ka? Haka isma’il ya ji? Mutumin da ya so ta tun tana yar kauyen ta? Ya so ta tsakani da Allah ba dan wani abu da ta mallaka a jikin ta ba, anya bata cuci kanta da rayuwar ta ba? Dafe kanta ta yi da yake barazanar tsinkewa, ta lallaba zuwa gaban mudibi ta tsaya tana sake kallon kanta da kanta! Duk in da ake so mace ta kai a haduwa da cika ta san ta kai, amma sai dai kash! ZAFAFA BIYAR!!! DUKKA LITTAFAN AKAN NAIRA DUBU DAYA (1k) KACHAL IDAN KUMA DAYA KIKE SO (300) BIYU (400) UKU (500) HUDU (700) KARKU BARI A BAKU LABARI, DAN WANNAN SALON NA DABAN NE KUMA TAFIYAR MA TA DABAN CE! ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN HAFSAT UMAR KABIR ZENITH BANK 2270637070 SAI A TURA SHAIDAR BIYAN 07040727902 IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA 09134848107 KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI. MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI. SAI MUN JIKU MUTANEN AMANA!💃🏼💃🏼💃🏼 [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (29) ***Bin Baban yake a baya ran Baban a bace har zuwa wajen motar sa, dama mantuwa yayi ya dawo har ya ji maganar da Maman take, bude masa murfin motar akayi ya shiga, sannan yace Tariq din ma ya shigo driver kuma ya fita ya jira su a waje. "Yanzu ni zaka watsawa k'asa a ido Tariq? Na nema maka auren yarinyar nan yau shekara guda, mahaifin ta ya bani wuk'a da nama, haka yarinyar da ba haifan ta nayi ba, ta karbi abinda nazo mata da shi sai kai? " "Ba ki nayi ba Baba, na karba hannu biyu wallahi, nagode Allah ya saka da Alkhairi ya kara girma." "Idan har ba k'i kayi ba, wacce irin magana naji kuna yi da mahaifiyar ka?" Shiru yayi dan baya son fadin laifin Maman, girgiza kai Baba yayi yace "Shikenan, kar naji kar na gani, ka fara shirye-shiryen daukar matarka." "In sha Allah Baba,kuma dan Allah ayi wa Mama uzuri,zan yi kokarin fahimtar da ita in sha Allah." "Mahaifiyar ku bata son gaskiya Tariq, uzuri nayi mata sau nwa ma, amma shikenan, kuyi magana da ita, Allah yayi maka albarka." "Amin." Ya amsa, sannan ya fita daga motar driver ya shigo, yaja suka fice daga gidan tare da motocin DSS dake bin bayan Baban. Wajen wasu kujeru ya nufa ya zauna, baya son wannan matsalar ta shafi zaman iyayen sa, dan haka ya zama dole ya karbi yarinyar ko da na wucin gadi ne, dan ba zai so akanta iyayen sa su dinga samun sabani ba. Yana zaune a wajen Fauwaz ya fito ya hango shi, sai ya taho ya zauna a gefen sa, dan be yi tunanin Tariq din yana gidan ba. Suna zaune iskar wajen na kada su, ta fito rike da hannun Usman da wata warmer madaidaciya, mayafi ta saka ta rufe kanta amma kana iya hango duhun gashin kanta, fuskarta fayau duk da k'asan zuciyar ta babu dadi, bata lura dasu ba, tafiyar ta kawai take kai tsaye zuwa part din Yaya, idanun sa akanta Fauwaz na ankare dashi, mikewa yayi ya nufe ta, ya kira sunan ta, waigowa tayi sai ta saki fuskar ta "Ya Fauwaz.." "Na'am, kin daina buyan?" "Dama ba buya nake ba fa." "Me kike?" Yace yana mika mata hannu, ta bashi warmer din hannun ta, mika masa tayi suka jera tana masa bayanin dalilin ta, wanda jin ta kawai yake amma ba wai ya gamsu bane. "Kinga Ya Tariq chan ya kafe mu da ido,kar ki juya just pretend kamar baki ganshi ba." "Dama ban ganshi ba ai, me yasa zai kafe mu da ido?" "Oho." Ya d'age kafada yana murmushi, share zancen tayi suka shige wajen Yayan yana kallon su, kamar ya tashi yaje ya kwankwashi kan Fauwaz haka yaji, ya rasa me yasa amma yadda yaga suna magana da murmushi yasa duk yaji haushi ya tik'e shi, cigaba da zama yayi a wajen har ranar da tayi saura ta karasa mamaye wajen, zafin ta ya bige shi. Mikewa yayi yana zura hannayen sa cikin aljihun wandon sa, yabi bayansu zuwa part din Yayan dan zuciyar sa ta gaza hakuri sai yaje yaga abinda yake faruwa. Dariyar Yaya ya jiyo har da kyalkyalawa tun kafin ya ida shiga ciki, daidaita fuskar sa yayi zuwa yanayin da ya saba a ko da yaushe, ya shiga da sallama amma ciki - ciki,dakatawa Yaya tayi da dariyar dama video take kallo a wayar Fauwaz na abin dariya. "Malam Badamasi an karaso?" Tace tana dariya, dariya Fauwaz yayi Jidda kuma ta dauke kanta zuwa wani shashen falon, zama yayi yana zaro hannun nasa yana kallon wajen da take zaune, kallon kallo Yaya sukayi wa juna ita da Fauwaz kafin su kwashe da dariya, dariyar da ta saka Tariq din tsarguwa. "Ina kwana?" Yace "Lafiya lou wallahi, kamar yadda ka ganmu ni da mutanen amana ta." "Ke bakya gaida mutane ne?" "Wai Jidda, ai bata son yawan magana kasan, kuma dai idan jinin ta be hadu da na mutum ba, bata masa magana ko Jidda?" "Haka ne kuwa." Fauwaz yace, "Ok yayi kyau ai, ni dai Yaya karki manta da alkawarin da mukayi." "Ina zan manta? Ka jira lokacin dai." "Shikenan." Yace yana maida kansa jikin kujerar , mikewa jiddah tayi, ta gyara yafen mayafin ta, ta ce "Yaya zan dawo anjima." Jan numfashi yayi ya sauke da sauri, yadda muryar ta, ta doki kunnen sa. Hada ido sukayi, tayi saurin janye nata tayi hanyar fita da dan saurin ta. Kundin tunani ya fada bayan fitar ta, sai ya mike kawai be ce uffan ba, ya fice daga shashen. Tafawa Yaya sukayi da Fauwaz, "Kaga mutumin ka ko?" " Wallahi Yaya, ke ai legend ce kinsan ta kan tsiya, wallahi ya Tariq ya fara bani tausayin dan yadda yake jin kansa da miskilanci jiddah oga ce, kuma tana da gudun zuciya tunda taji da bakin sa yana furta wannan maganar zaa sha wuya kafin ta dawo daidai." "Su karata chan, idan suka tare zasu daidaita kansu, mu dai muyi iya yinmu mu hora shi sosai, sauran mu barwa jiddaa su karata." "Kin san ta kan tsiya Matar nan." "Dani yake magana ai, kunno min kallon nan na cigaba." "An gama ranki ya dade." Kunna mata yayi yace zai je ya dawo yanzu, yana fita ta sa hannu ta jangwale kallon gashi bata iya ba, haka tayi ta tabe-tabe har tazo kan video da yayi mata a airport da za'a chanja ta daga mota zuwa jirgi, a cikin jirgin har zuwa gida. Salati ta rafka wayar saura kiris ta subuce daga hannun ta, sai gashi ya dawo yana shigowa ta damke masa hannun riga "Ni zaka yaudara? Wayyo Allah." Sai ta fashe da kuka "Menene Yaya? Me ya faru?" "Ubanka ne, wallahi sai yazo da kansa ya raba ni da kai yau, sai da nace maka bana so, bana so, amma saboda ka raina ni..." "Wai menene Yaya?" Ya yi dabara ya zame rikon da tayi masa ya karbi wayar sa, "Waye ya saka ni a jirgi? Waye idan ba kai ba? Waye?" "Auw wai magaanar jirgi ne Yaya? Yaushe kika shiga ni bansan zancen ba." "Video din menene a wayarka? Ni zaka rainawa hankali?" "Video ni? Yaushe akayi? Bansan maganar me kike ba fa Yaya." "Idan yazo sai kayi masa bayani, ita Jiddan zTa shigo ne wato har da ita za'a hada baki a kassara min rayuata?" "A ah fa, ba laifin jiddaa, tunda dai kin riga kin ga video din ba amfanin boye miki, maganin bacci na baki aka saka ki a jirgin." "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Wayyo ni Hajara, ni kake so kaga baya ko? So kake ka kashe ni, na shiga uku na lalace Wayyo." Gwalo yayi mata, ya fice da sauri tana kiran sa ya gudu yana dariya. Kuka ta shiga yi wiwi tace Usman yaje ya kira mata Anty, yaje zai gasu sun dawo tare da saurin ta, tana zuwa tace ta kira mata Baba yazo yanzu yanzu Fauwaz yana son ganin bayanta, duk yadda Aunty taso ta tsaya suyi magana ta fahimci me ke faruwa amma kemaimai taki sai kuka take tana fece hanci, Baba yadda Aunty ta iya dole ta kira Baba be dauka ba dan dama yace suna da meeting, hakuri ta dinga bawa Yayan har ta samu ta lafa da rikicin, ta lallaba ta, ta zauna taje ta kawo mata kunun ta tasha ta kunna mata kallo, sannan ta samu ta bar maganar kafin Baba ya dawo. Tana zuwa daki ta cire mayafin ta jefar akan gado ta kwanta rigingine, duk yadda taso ta danne abinda yake cin ranta ta kasa, gashi bata so Aunty ta sani dan zata shiga damuwa ne, kuka take so tayi amma ta kasa,sai ta dauko wayar ta, ta kira Safeera duk a kokarin ganin ta dauke hankalin ta baki daya, sun jima suna hira kafin suyi sallama, ta samu relief sosai duk da ba maganar sukayi ba, amma dai a kalla ta samu wadda zasuyi hira har ta fahimce ta. ***Tun bayan ya baro wajen Yayan ya fice daga gidan, dan yana da abubuwan da zai yi masu yawa kafin ya fara aiki sosai dan tuni yayi accepting din offer din Air Canada, one of the best airlines in Canada. Aikin pilot yana bukatar time and dedication, with alot of commitments duk da haka dai shine burin sa, yanzu haka zuwan nan da yayi jinsa yake a takure, ya saba ko yaushe suna sama kamar tsuntsaye. Yana hanyar dawowa Mama ta kira shi, ya daga yace mata baya gidan dan baya son haduwar su a dan wannan lokacin, dan baya son matsala tsakanin ta da Baba, yafi so ta kwantar da hankalin ta, shi zai yi abinda ya kamata. Yana shigowa gidan suna kokarin komawa wajen Auntyn ita da Amira, a gaban su yayi parking bayan ya haske su da hasken fitilar motar, bud'e murfin yayi ya fito be ko kashe motar ba, Amira ta gaishe shi da sauri, ya amsa yana jiran yaji itama da gaishe shi, amma sai yaga ta share tana kokarin cigaba da tafiya dan barin wajen, ransa ne yaji ya baci, dama ga haushin abinda Yaya tace dazu wai idan jinin mutum be hadu da nata ba, bata magana, baya son raini sam me yasa ba zata gaishe shi ba, me yasa ba zatayi masa magana ba. Ganin tana kokarin barin wajen dan har tayi taku kusan uku ya sakashi sa hannu ya damko nata hannun ta, kamar wanda aka jonawa shokin haka suka ji a lokaci daya, ya kafe ta da idanun sa dake sata diriricewa "Me..ne.. ne?" Tace a duburburce, "Rainin hankali." Yace a hankali, bata ma san me tayi ba? "Dan... Allah ka cikani zafi." Ta nuna masa hannun nata da ido, dan sassauta mata rikon yayi,ya cigaba da kallon ta, shi sam yanayin da take zarya a cikin harabar gidan dake cike da ma'aikata da mutane mabanbanta shine be yi masa ba, ba kuma wai kishi yake ba, kawai dai be ga amfanin hakan ba tunda dai ai ko ba ya son auren dai amma akwai igiyar sa akanta, yanzu ma mayafi ne yalolo a iya saman kanta, duk da kayan jikin ta basu da aibu amma baya son hakan, ko su Fauwaz ne baya so suna mingling ta bari idan aka warware auren nasu sai tayi duk abinda ma taga dama be damu ba. Tuni Amira ta cikawa wandon ta iska, dan ta lura Ya Tariq din ma ya manta tare suke da Jiddan, sake maimaita ya cikata tayi tana kauda fuskar ta, dan ta rasa dalilin da yasa yake shigar mata rayuwa, tana iya kokarin ta na ganin tayi nesa dashi amma yana sake shigowa yana dagula mata lissafi "Anki a cikakin." Yace yana hade rai, kokarin kwace hannun ta shiga yi, wanda ko zaa hada irin ta goma basu isa su kwace ba, dariya ma ta so bashi yadda take ta kicin-kicin kwace hannun nata, sai zuciyar sa ta raya masa wani abu, be yi dogon tunani akai ba, kawai ya bi umarnin zuciyar tasa, ya jata ya bud'e murfin motar ya tura ta a ciki, ya shiga ya juya ya sake ficewa daga gidan. Uffan bata ce masa ba, ya dinga gudu da ita akan titin, kanta na kallon window lokaci zuwa lokaci tana saka hannu ta share kwallar da take zubo mata. So yake ta bude baki tayi masa magana, ta roke shi ya tsaya ko tace ya maida ita gida amma kemaimai taki cewa komai, kamar zai yi hauka haka yake ji, be taba ganin miskilanci irin wannan ba, duk yadda ake fadan nasa ta taka shi ta shanye dan shi ya rage kusan kaso goma a ciki bayan tafiyar sa. Gajiya yayi da zagayen ya samu gefen wani restaurant yayi parking, suka zauna a motar kawai, zaman da ya haifar masa da wani yanayi me wahalarwa. Karkata zaman sa yayi ya juyo yana kallon wajen da take zaune, ita kuma tana kallon waje taki yarda ko sau daya ta kalli ciki dan zuciyar ta, tayi masifar yin weak. "Jiddaa..." Ya samu kansa ta kiran sunan ta, wanda shi kansa be san dalilin kiran nata ba, kasa amsawa ba kuma wai dan tana sani ba, sai dan ba zata iya amsa masa ba, tana bud'e baki kuka ne zai fito, ita kuma bata so yaga gazawarta. Dunkule hannun sa yayi, ya daki sitiyarin motar, sautin kukan ta ya shigar masa har cikin kwakwalwar sa, baya son kukan ko kad'an, kuma be ga wani babban dalili da zai sakata kuka ba, tunawa yayi ranar da ya ganta a kitchen tana kukan nan, tabbas akwai babban abinda yake damunta, toh ko bata son shi ne? Sai yaji gabansa ya fadi, tsoro ya shige shi. Cigaba da kukan tayi a hankali bata san yana jin ta ba. Ji yayi kamar ana fuzgarshi zuwa gareta, ya dinga matsawa har ya matso daf da ita, har tana jin hucin numfashin sa, hade da kamshin turaren sa da ya kara karfi saboda matsowar da yayi kusa, bata san haka ya zo daf ba, ta juyo da nufin ganin abinda yake yi, ba tare da tunanin komai ba, ya rungumeta yana zagaye ta da hannun sa zuwa cikin fafffadan kirjin sa. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (28) _INA MASOYA KUMA MA'ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._ _TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_ _A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_ _SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_ _AKWAI TURAREN *AL'AJABU NA TSUGUNNO DA KHUMRAH* DIN SA_ _SANNAN SU NA DA *TURAREN GASHI NA CREAM DA KUMA SPRAY DIN SA NA FESAWA*_ _BA ANAN SUKA TSAYA BA. SU NA DA *TURAREN MOPPING, DA NA BANDAKI AKWAI NA RUWAN WANKI DA NA FESAWA A DRAWER KO AKWATI*_ _AKWAI KAYAN GYARARRAKI NA FATA. KUJERAR TSUGUNNO, KASAKE NA WUTA, COAL IGNITER TA KUNNA GARWASHI, ELECTRIC BURNERS DA ENGLISH COAL_ _AKWAI LAFFAYAS DA SAURAN TURARUKA NA KAMSHI KALA KALA_ _SU NA BADA KAYAYYAKIN SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYA AKAN DAYA DAYA. SANNAN SUNA TURA KAYAYYAKIN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE. KAYAN SU YAN CHADI NE DA SUDAN DA KUMA YERWA WATO MAIDUGURI._ _KYAU, INGANCI DA RAHUSA SAI KAYAYYAKIN KAMFAMIN YERWA INCENSE AND MORE. SAI KUN GWADA ZAKU BAMU LABARI_ _NAMBAR TARHON SU DA ZAA KIRA KO MUSU MAGANA TA WHATSAPP ITACE: 08095215215_ _INSTAGRAM HANDLE DIN SU: @yerwaincense_and_more_ _YERWA INCENSE AND MORE: A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS AND MORE_ ***Kamar wanda aka dasa a wajen haka ya tsaya k'yem, tun da yake, tunda yake a rayuwar sa be taba ganin gashi irin wannan ba, yana yawan imagining mace da long hair amma not this long, daga ganin shi zai yi dadin tabawa. Sam bashi da cika bare yawa, sai tsayi da tsantsi da baki. Yana tsaye yana shawarar abinda ya kamata yayi, duk da ya gaza gasgata zuciyar shi cewa ita ce, that slim girl da yake ganin ko motsi tayi da yawa zata iya ballewa, duk da hr yanzu she's slim amma kuma she's curvy, irin yadda yake so da muradin matar da yake so, amma kuma ba wai son ita Jiddan yake ba, kawai dai she possess some qualities da yake so a wajen mace. Tunawa yayi da bata ko gaishe shi ba, bare ta bude baki tayi masa magana sai ma wuce shi da tayi kamar bata lura da existence dinsa ba, ransa ne yaji ya baci, ya bar kofar ya nufi hanyar da tabi ya tarar da daki daya a wajen, ya tabbatar nan ta shiga, knocking yayi a kofar jidda dake durkushe a wajen tayi saurin kallon kofar, tunanin ta Aunty ce, tayi saurin saka bayan hannun ta, ta goge fuskarta sannan ta bud'e kofar tana sauke kanta k'asa kar Aunty ta gano wani abu. "Baki iya gaisuwa ba?" Yace bayan ya sake kare mata kallo, da sauri ta dago ta kalle shi, taga ya zura mata ido, saurin dauke kanta tayi bata ce masa uffan ba "Kina kallo na, amma ko ki gaishe ni, ko ba'a koya miki gaisuwa bane?" Nan ma dai shiru tayi masa, hakan ya sake kular dashi, ya fizgo hannun ta, tayi saurin janye wa tayi baya da sauri, ya samu damar shigowa dakin yana kallon ko ina a cikin dakin, idon sa ne ya sauka akan abincin dake saman bedside drawer, ya nufi wajen ya dauki tray din, ya samu waje daga gefen gadon ya zauna ya shiga cin abincin yana kurbar lemon kwakwan yana satar kallon ta, tana tsaye a wajen da take bata motsa ba, bata kuma ce masa ci kanka ba, yaci abincin sa ya koshi yana ci yana more kallon ta, ba tare da ta sani ba, haka shima ba tare da ya san abinda yake ba. Tunanin sa ne ya kawo masa, ya tuna me ma yake a cikin dakin ta, baya son raini kwata-kwata, sai gashi yana kokarin siya ma kansa raini da kudin sa, ficewa yayi be sake ce mata komai ba, tayi saurin rufo kofar yana fita, yaja dan siririn tsaki ya fice daga part din. *** A zaune ya samu Fauwaz yana waya, ya watsa masa wani kallo yayi wucewar sa bedroom din sa, saurin katse kiran Fauwaz yayi, ya tashi yabi bayan sa, ya tarar dashi yana cire kayan jikin sa "Ina ka shiga ne? Tun dazu nake jiran ka gashi wayar ka, ka barta a nan." "Ina ruwan ka da in da naje? Yace yana rataye rigar sa a jikin hanger ya rage saura singlet kawai da dogon wandon "Na zata wallahi ba zaka dawo yau ba, ina ta tunani gashi Mama tana ta jiran ka." A gabansa ya tsaya bayan ya jawo towel sabo daga cikin closet dinsa, ya rataya a kafadar sa "Yanzu ace har da kai, za'a yi min irin wannan auren a rasa wanda zai fada min." "I'm very sorry, amma kaima kasan babu wanda yake going against maganar Baba, kuma kai ba kowa ma kake kulawa ba ko da a family din su Mama ne, da nasan definitely wani sai ya fada ma, mu kuwa ba zamu ketare maganar Baba ba, har Mama da taso nuna bata so sai da suka samu matsala akan haka." "Akan auren?" "Yes, akan auren wallahi." "This is serious." "Shiyasa nake so ka tsaya muyi magana, duk da naga dazu ranka ya baci sosai, amma nasan ba zai yi lasting ba, just hear me out." "There is no need ai, Baba ya fada min komai, so ka barshi kawai." Sai ya juya yayi shigewar sa toilet, dan ji yake kamar ya shekara be wanka ba. Yana wankan yana tunanin fuskar ta, wadda ta tsaya masa a ko ina, mamakin kansa yake yi, har ya gama wankan ya dauro alwala ya fito, ya shirya cikin kayan baccin sa, ya feshe jikin sa da turaren Versace collection, ya fito falon ya dauki wayar sa ya sake komawa ciki ya rufe kofar ya rage hasken dakin zuwa me duhu, yayi relaxing akan couch ya kunna datar wayar sa yana so ya duba Ishaq. Ya dan dau lokaci akan wayar yana kallon messages din Yasmin na popping a saman wayar ya share be duba ba, ya saka wayar a flight mood ya kwanta bayan ya karo karfin A C din dakin saboda yadda yake da jin zafin gaske, gashi ya saba sosai da yanayin sanyin kasar da ya baro. A tunanin sa yadda ya dauko gajiya yana rufe idon sa bacci zai dauke shi, amma sai ya samu kansa da kasa baccin kwata-kwata, ya runtse idon sa ya bude amma still baccin yaaki zuwa kemaimai. Mikewa yayi ya kunna hasken dakin ya fito da system dinsa domin ya samu ya mantar da kwakwalwar sa tunanin da take ta kokarin turo masa, ya dade nan ma amma babu wani progress, tunanin ta ne yake neman damun sa, dan ko dan runtse ido yayi sai ya hango ta, a tsaye a kitchen din nan tana jan ajiyar zuciya, duk da be san dalilin kukan nata ba, amma ya taba shi sosai, wanda har yake jin da ya sani ya tambaye ta dalilin kukan nata, duk da baya jin akwai wani abu da zai iya mata bayan tambayar. Tunawa da yayi be yi shafa'i da wutri ba, yasa shi kashe system din da saka ran kila dan be yi bane yasa ya kasa bacci amma yanzu tunda ya tuna yana idarwa yasan zai kwashe shi baccin. Da wannan tunanin yayi sallar ya sake kwantawa amma dai still ba wani progress, tsaki yaja ya zura slippers dinsa ya fito, ya wuce Fauwaz a falon yana wani aikin cike cike a system, ya bishi da ido har ya fice. Harabar gidan tana nan kamar rana saboda hasken da ya mamaye ilahirin gidan, be san dalilin da ya fito dashi ba, be kuma san wajen wa zai je ba, ya samu kansa kawai da hakan ya dinga zagaye compound din kamar me gadi, idanun sa na kan part din zuciyar sa na fizgar sa akan ya je, ya shiga amma ya daure, sai da ya gaji da zagayen sannan ya koma ciki ya sake dukunkunewa a cikin blanket, ya samu da k'yar baccin ya dauke shi bayan ya cika kansa da tunanin ranar da duk wani abu da ya wakana a ranar. ***A makare ya tashi dan saura kiris ya rasa sallah a masallaci, dan sau biyu Fauwaz na tashin sa amma ya kasa tashi sai da yaji da gaske idan be tashi ba zai rasa sallar sannan ya taso yayi alwawar a gurguje yafita zuwa masallaci, ana sallar ya dawo daki saboda wani irin bacci da yake ji. Yana kwanciya ya koma baccin wanda har sai da rana ta daga sosai sannan ya tashi, shi din ma aiken Mama ne ya sashi tashi dole dan ta matsu yazo taji yadda aka kare duk da bata taba tunanin akwai wanda zai masa maganar nan a jiyan ba ganin ya dawo kuma ya gaji, ta san kuma basu hadu da Baba ba dan late Baban ya dawo. Wanka yayi a gurguje, ya nufi part din Maman, ya tarar da abincin sa achan ya dan yi breakfast din sama-sama sannan suka zauna da Maman ta dan bugo cikin sa dan taji yadda ake ciki "Akwai wata magana da kukayi da wani bayan dawowar ka ne?" "Magana?" Yace kamar me nazari, "Eh kamar maganar aure haka ko wani abu." "Oh eh, Baba yayi min magana." "Yace maka me? Yaushe ma kuka hadu dashi?" "Jiya very late, yayi mun maganar." "Ina fatan baka amince masa ba, dan nasan babu abinda zakayi da wannan yarinyar me kama da sadakar yalla, kafi karfin ta nesa ba kusa ba, saboda haka bana so, ban amince zaman ku a karkashin inuwa daya ba." "Mama?" "Kwarai da gaske bana son auren, karfi na kawai akafi dan an hada ni da mahaifin ku,dan haka tunda kai na isa da kai, inaso ka sakar musu 'ya, dan bana kaunar ta ko miskila zarratin wallahi,idan yaso koma wace sai ka samo kuyi auren ku". "Tunda ba kya son ta sai ki hanata numfashi Aisha." Mikewa tayi Tariq din ma ya mike da sauri suka kalli kofar da Baban ya shigo, kofar baya da ya saba shigowa part din. Da safe Mama taji fitar sa dan da wuri ya fice daga gidan bata kuma zata ya dawo ba, kunya ce ta lullube ta, ta rasa in da zata saka kanta dan ba haka taso ayi ba, ya akayi ma bata ji bud'e kofar ba sai shigowar sa kawai "Nace tunda bakya son ta, sai ki katse mata numfashi." Hanyar ficewa Tariq ya nema, Baba ya buga masa tsawar da tasa shi kasa kara ko step daya "Wallahi wallahi wallahi, kaji rantsuwar dan musulmi ko? Wallahi ka kuskura, ka saki Hauwa'u wallahi babu ni babu kai, kaji na fada maka." "Ayi hakuri Baba." Ya russunar da kansa k'asa "Ke kuma, ko ciwon kai Hauwa'u tayi sai na tuhume ki, dan bazan kara yarda dake ba, ni ne ubanta dan haka zan yi duk yadda zan yi na kare ta daga sharrin ki, mutuniyar banza." K'ala Mama bata ce ba, ya juya ya fice Tariq ya bi bayan sa da sauri [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (30) ***Wani abu yaji tunda tsakiyar kansa har zuwa tafin kafarsa, yaji kamar duniyar na juyawa baki daya a tsakankanin su, su biyu kadai, kokarin zare jikinta take ya matse ta sosai ya hana mata ko da kwakkwaran motsi. Lamo tayi tana jan numfashin kadan-kadan. Bugun zuciyar ta ne ya hadu da nasa, har tana iya jin yadda tasa ke beating very fast kamar wanda yayi gudun tsere. "Why are you always crying?" Yace cikin muryar sa da ta shiga chan ciki, bata amsa ba, sai dan motsawa da tayi kad'an ya sake kankame ta "Tell me? Ba kya son auren?" Wani irin faduwa gaban ta yayi, ya cigaba da magaanar cikin kunnenta "Nima bana so... So ki daina kuka zamu samu hanyar da ba zamuyi hurting iyayen mu ba, I promise you." Baki daya tunanin ta ne ya tsaya na dan dakiku, taji gaba daya duniyar na juya mata, a tunanin sa saboda bata son auren take kuka? a tunanin ta kuma ta dauka he's ready to accept her, a tunanin ta ba zai iya furta mata baya son auren ba duk da bata da yakinin dama yana so din, a karo na biyu ya sake breaking heart dinta, into pieces. Fizge jikin ta tayi da karfin gaske, ta matsa daga jikin motar ta juya masa baya. Kallon bayan ta yake yana jin duk babu dadi. Kukan ta cigaba da yi yana jinra, yana jin wani irin zafi a cikin zuciyar sa, be san meyasa kukan yake taba shi ba, duk da dama shi a rayuwar sa ya tsani yaga mace tana kuka, kallon su yake a matsayin wasu weak mutane da kukan kawai zai iya haddasa musu babban al'amari. Zuciyar ta ce ta dake, taji a lokaci daya kukan da take ya dauke, taji bata son sake ko da minti daya ne a zaune a cikin motar, babu amfani, kwata-kwata babu amfanin cigaba da kukan ta, duk da tasan da gasken gaske take son shi, amma kuma babu amfani tunda shi baya so, zata sakawa zuciyar ta salama ta karbi duk wani abu da yazo mata, ba zata sake bata hawayen ta ba, balle murfin motar tayi, zata fita yayi saurin fincikota, ya rike ta k'akam yana saka idon sa acikin nata "Menene matsalar ki?" Ya fada yana zagaye idanun sa a kan fuskar ta "Ka kyale ni dan Allah." "Me yasa? Tell me? Ki bud'e bakin ki, kiyi magana." "Gida nake son zuwa." Tace tana kauda kanta gefe ganin yadda yake motso da fuskar sa daf da tata. "Zaki je gidan, just tell me menene yake saki kuka? Are you sick? Baki da lafiya ne?" Girgiza masa kai tayi "Toh menene? Tell me dan Allah..." "Ba komai, ni ka kaini gida." "Ba zan kaiki din ba, anan zamu kwana babu in da zaki." Kallon sa tayi ya gid'a mata kai, kwace hannun ta, tayi ta motsa kafarta tana kokarin sauka yace "Idan kika fita wallahi sai na baki mamaki." Kamar bata ji ba, ita burin ta kawai ta je gida, ta gaji da zama waje daya dashi knowing fully baya son ta, he's just concern akan kukan da take, which yake tunanin ma son auren ne bata yi shiyasa. Folding hannun sa yayi yana kallon ikon Allah, ta sauka daga motar tayi gaba. Da sauri ya fito daidai lokacin da wata mota ta haske ta, ya hango gashin kanta ta dan mayafin dake kanta da ba wani na kirki ba da wanda ya bayyanar da kusan gashin kanta, wasu maza sake kusa da ita suka kalle ta, da saurin sa cikin baci rai ya riko hannun ta, ya shiga janta zuwa motar, ya turata ya danna lock sannan ya koma ya shiga cikin motar, yaja suka bar wajen. Kukan ta cigaba da yi masa, ransa ya sake baci sosai, ya dinga gudu sosai a titin ya dauke hanyar gidan, kanta na k'asa har suka karasa in da zasu, yayi parking sannan ya zura kansa baya ya bud'e ledar kayan da ya siyo dazu, ya dauko jacket din sa, ya zauna sosai sannan ya dora mata ita a saman bayan ta, dagowa tayi idanun ta da sukayi ja sosai ya kalla sai ya kauda kansa, ya shaki iska ya fezar da bakin sa, sannan ya juyo yana tamke fuskar sa sosai, ya dauki rigar ya bude ta, ya sa hannu ya janye mayafin dake jikin nata, ta kalle shi da sauri ya dalla mata harara ya shiga saka mata rigar akan doguwar rigar dake jikinta, ya balle botir biyu na jiki ya bar sauran, sannan ya dauki mayafin ya nannad'a mata akanta, ya sake zagayo dashi ya rufe kan nata, ya d'an ja baya ya kalle ta kad'an sannan ya zagaya ya fita ya bude mata. "Fito." Yace yana kauda kansa gefe Kallon wajen tayi, ta ki fitowa, "Fito nace kafin ranki ya baci." Yayi maganar still yana kallon gefe, share hawaye tayi, ta zuro kafafunta ta fito, ta tsaya a gaban sa, yar karama sosai akan sa, bata fi ya hadiye ta ba "Strong head." Ya furta sanda ta tsaya a gabansa kanta na k'asa. Hannun ta, ya kama cikin nasa, ya shiga takawa zuwa cikin building din, wanda yake dauke da tsirarun mutane saboda yadda lokacin ya dan fara ja, reception yaje ya karbi key ba tare da yace komai ba,suka haura sama ya ciro key ya saka a jikin kofar ya bud'e,suka shiga ciki ya maida kofar ya rufe. Guest house din Baba ne, anan yake saukar duk wasu bakin sa, daki ne babban gaske, me dauke da madaidacin gado, tv, fridge da yar madaidaciyar wardrobe. A jikin kofar taja ta tsaya,yayi gaba abin sa ya zauna a gefen gadon yana zaro wayar sa, tun dazu yake jin kiran amma yaki dagawa saboda baya son yin magana a yadda yake jin sa. Ta gefen idon sa ya kalleta tana tsaye a jikin kofar ya dauke kansa, yau sai ya kure ta duk miskilancin ta kuwa, kuma sai ya nuna mata shi din gaba yake da ita ba daidai suke ba, shiyasa ya fasa komawa dasu gidan, yaga yadda zatayi yasan dole a karshe ta magantu,daga nan sai ya maida ta din. Tsawon lokaci tana tsaye a kofar har kafarta ta fara sagewa, kamar be san da ita a wajen ba yadda ya dinga sabgogin sa, zamewa tayi ta zauna kawai a wajen ta hada kanta da guiwar ta. Tashi yayi ya duba time yaga sha daya har ta kusa, sai ya shiga toilet ya dauro alwala yazo yayi akan dan madaidacin carpet din dake wajen, ya idar ya haye kan gadon ya kwanta bayan ya kashe hasken dakin ya zama sai kad'an Dagowa tayi tana kallon wajen da yake a kwance, da gaske yake kenan ba zai maida ita gida ba, me zata ce wa aunty? Gashi bata fito da waya ba balle ta kira, tana nan a durkushe a wajen cikin zulumi gashi ta gaji da kukan da bata san ma'anar sa ba. Shiru tayi cikin tunanin me ya kamata tayi, sai kawai ta yanke daukar wayarsa ko text ne ta turawa aunty, duk da tasan kila Amira ta fada mata amma tasan dole zata damu da bata dawo ba, ita duk nauyi da kunyar Auntyn ma take ji amma dole sai ta kira ta ko text message. Tashi tayi sad'af-sad'af ta nufi wajen da yake kwance, dama a gefen sa ya ajiye wayar, ta kai hannun ta zata dauka ya damke hannun yana bud'e idon sa, suka had'a ido da sauri tace "Aunty zan kira." Kallon bakin ta yayi, yaki sakin hannun ta, ya jawota jikin sa gaba daya yana matse ta, ya shiga wajen kiran ya kira Aunty duk da bashi da tabbas din batayi bacci ba a lokacin, kira daya ta dauka kuwa, yayi sallama ta amsa "Aunty afwan na tashe ki kina bacci." "A ah ban ma kwanta ba Tariq." "Ok dama wannan ce take so zatayi miki magana." "Jidda wai, ba komai mayi magana da safe kawai." Bata jira yayi magana ba ta kashe wayar, "Kinga ni ko? Aunty ko yanka ki nayi na cinye ba zata ce min komai ba." Ya rad'a mata a kunne, muskutawa tayi ya sake jawota yana hade ta da jikin sa. "Ki yi bacci kawai dan ba tafiya zamuyi ba, ki barni zan samo solution yadda za'a yi, sai ki daina kuka dan an aura miki ni." Daga haka be sake ce mata komai ba, ya rufe idonsa yana jin wani irin nutsuwa na saukar masa. Rufe idon ta, tayi kamshin turaren sa na cikata, tayi luf ko kwakkwaran motsi ta kasa yi, tana jin shi ya soma jan numfashi, alamun ya fara nisa a cikin baccin sa, kallon fuskar sa dinga yi, a hankali a hankali abinda take ji na rashin nutsuwa ya dinga gushewa, wata nutsuwa na maye gurbin sa. ***Idan tace ta san lokacin da bacci ya dauke ta, tayi karya, bacci tayi sosai irin wanda ta dade bata yi irin sa ba. Bangaren Tariq din ma haka ne, bacci yayi peacefully har yaso ya makara tashi. Shi ya fara farkawa ya dan janye jikin sa yana kallon fuskar ta, very cute da dan karamin lips dinta da ya dace da yar fuskarta. Duk da ta chanja masa sosai amma shi har yanzu kallon baby yake mata, dan a yanzun ma yar karama ya ganta a gabansa. Samun kansa yayi da yin murmushi ya tashi yaje yayi alwala yazo daidai saitin kanta ya shafa mata ruwan hannun sa a fuskar ta, da sauri ta bud'e idon ta, ta tashi zaune tana zazzare ido, tamke fuskar sa yayi, ya wuce gaba zuwa wajen da zai yi sallah, tashi tayi ta shiga toilet din tayi alwalar itama ta fito ta tsaya tana tunanin da abinda zatayi sallah dan mayafin kanta babu yadda za'a yi yayi sallah. Yana zaune yana addu'a tunda ta fito, bata ce masa komai ba shima be ce mata ba, tana ta tsaye har ya gama ya taso yazo ya kwanta yana kulle idon sa "Za.. n..yi.. sallah." Ta fada a rarrabe kamar me jin tsoro "Yi mana." Yace still idanun sa na rufe "Mayafi na ba zai ba." "Kinsan ba zai sallah ba amma kika yafa kattin banza da wofi suna kallanki?" Ya fada a hasale tunowa da abinda ya faru jiya "A cikin gida ne ai." "Cikin gidan babu Maza? Ko muharraman ki ne? Eh?" Yace yana tashi zaune, shiru tayi ganin daga magana har ya harzuko, kwafa yai ya tashi ya fita ya sauka kasa, ya samo mata madaidacin mayafi a wajen ma'aikata wajen, ya kawo mata ta yafa a kasa tayi rolling da nata, sannan tayi sallar. Ta zauna a wajen har gari yayi haske sosai, yana ta baccin sa hankali kwance. Baki daya hankalin sa yayi gida, tana ta sake-sakn ko ta gudu ne sai gashi an kirashi, ya sa hannu ya kashe kiran aka sake kira a karo na biyu, sai da ya dan ja tsaki sannan ya daga yana kara wayar a kunne "Hello..." "Tariq kana ina ne wai?" Muryar Mama ta fito ta cikin wayar har tana juyowa daga in da take zaune, dan bude idon sa yayi ya murza kansa cikin yanayin baccin dake kansa yace "Bana gidan Mah, anjima zan shigo." "Da gaske ne kenan" tace gabanta na faduwa dan taji Amira da Fauwaz suna maganar kasa -kasa "Me?" "Ba komai, kazo gida kawai inason ganin ka." "Shikenan, I'm on my way." Ya katse kiran yana leko ta daga wajen da take zaune, ya d'an ya mutse fuska ya mike tayi saurin dauke kanta zuwa dayan side din, kamar be gani ba, ya shiga ya gyara jikin sa ya fito yace ta taso, da sauri ta mike har tana kusan bashi dariya. ***Mama na compound din zata fita Tariq din ya shigo, idon ta akan motar tana son gasgata abinda take gani, Jidda ce a zaune kusa dashi, jiri-jiri taji yana neman kayarda ita, kafin ma su gama parking tayi saurin shigewa ciki dan bata jin ko fitar zata iya a lokacin kuma. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (31) ASSALAM ALAIKUM DEARIES BARKAN KU DA KOKARI…. KAMAR KODA YAUSHE. WANNAN KARON MA MUNA BARAR ROKON KU WAJEN TEMAKAWA CHANNEL DIN SUDEIS DAKE MANHAJAR YOUTUBE YARO NE DAYA TASHI DA SON KARATUN ALQURANI ME GIRMA. YA KE KUMA KWADAYIN GADON ME SUNAN SA SHEIKH SUDEIS. DAN ALLAH A TEMAKA A DANNA MASA SUBSCRIBE. A KUMA YI VIEWING DA LIKING. A TEMAKA DA SHARING MA... JAZAKUM ALLAH KHAIRAN AS YOU DO... " Assalamualaikum dear sisters and brothers. Welcome to ummu sudais YouTube channels? A channel where the Holv Quran is been recited from different Angles. Click on this link and listen to the Beautiful recitation that will melt your heart https://youtu.be/Lafgc749sK8 Your subscription to our channel is of Great important. Please help us grow our channel by subscribing and liking **** Da sauri ta bud'e motar ta fice ya tsaya yana kallon ta, hadda d'an gudun ta, ta bude kofa sai ta waigo ta kalli wajen da yake, ta jujjuya bakin ta sannan ta shige da sauri, murmushi yayi ya rufe motar ya nufi bangaren Maman yana jin sa sakayau kamar wanda ya sauke wani baban nauyi dake kansa. A tsaye ya samu Maman tana kaiwa da komowa a tsakanin hadadden falon nata, tun kafin ya gama shigowa ta soma fada "Ni zaka wulakanta Tariq? Ni?" "Mama... Me ya faru?" "Tambaya ta kake me ya faru? Baka san me ya faru ba Tariq?" Girgiza kai yayi "Allah Mama ban sani ba." "Menene hadin ka da yarinyar nan?" "Mama?" "Eh menene hadin ka da ita? Daga ina kuke ma tukunna? Kar dai kace min? Noo ba zai yiwu ba." "Dan Allah ni dai Mama ki kwantar da hankalin ki." "Ya zan kwantar da hankali na wai? Hu? Taya kake so na kwantar da hankali na ina ganin ku tare? Kasan abinda hakan ke nufi? Na rasa ka kenan,." "Ba zai lasting ba mama, just give me sometime, bana so akai na ku samu matsala da Baba." _"I'm doing it for Baba."_ Ya fadawa kansa da kansa k'asa-k'asa amma sai yaji kamar zuciyar sa bata karbi uzurin sa ba, so yake dole ya karfafa kansa cewa duk ma abinda yake saboda a samu maslaha a tsakanin iyayen sa ne, shi he has nothing to do with her, ba daidai dashi bace sai ya karyarta ma ai, amma kuma sam zuciyar sa taki bud'e masa kofar da zai aje irin wannan uzurin da har zai samu wajen zama a cikin zuciyar tasa "Don't go far na gaya maka toh, Halima da yarinyar are cunning, idan baka yi wasa ba you will end up..." "Nooo Mah..." Ya katse ta "I don't think hakan zai faru, in sha Allah hakan ma ba zai faru ba." "I hope so, fita zan amma ganin ku tare na ji ma na fasa, we only have few days sai kayi duk yadda zakayi kafin a shiga cikin bikin, bana son kuma silly excuse dan ba zan karba ba." "In sha Allah." Yace amma kuma sai yake jin kamar ba zai iya aikata abinda Maman take so ba, amma kuma why not? Shi ai ba son yairnyar yake ba. Fita yayi ya nufi bangaren su, yaje yayi wanka sannan yayi breakfast ya zauna yana hutuwa a falon har Fauwaz ya shigo. ***Kamar munafuka haka ta shiga part din nasu, aunty na zaune a falon taji kamar ta nutse saboda tsabar kunya, kanta a k'asa ta shiga ciki, ta gaida Auntyn tayi saurin shigewa dakin ta, tasa key ta kwanta rigingine tana kallon pop, ta kasa tantance yanayin da take ciki gaba daya,ta kuma rasa a wanne mataki zata ajiye abinda Ya Tariq din yayi, tunda ya nuna mata time kawai yake jira yayi ending marriage din nasu, kila dai kawai so yake ya dagula mata lissafi ya barta da ciwo a zuciyarta, zatayi duk yadda zatayi ba zata sake bari su hadu ba, ballantana har wani abu makamancin hakan ya faru. Message ne ya shigo wayar ta sai a lokacin ta tuna da wayar, baki daya kamshin turaren sa take kamar wadda tayi wanka da ruwan turaren, duk ya cika mata kofofin hancin ta, wayar ta dauko ta shiga message din sai taga Ya Fauwaz ne _"I will take over daga nan, kamar yadda nayi miki alkawari Ya Tariq sai yazo da kansa ya kawo kansa wajen ki, ki barmun komai, ke dai kawai kiyi avoiding nasa."_ Murmushi tayi kawai ta goge text din, dan ita bata taba tunanin Tariq din zai yi abinda Fauwaz din yace ba, bata ki ba idan baya hayyacin sa ko kuma dai wani babban al'amari, itama tun farko tayi gangancin hada kanta dashi, banbancin su yayi yawan da zai yi wuya ya iya sakkowa zuwa level dinta. Har magriba tana kunshe a daki sau biyu Amira na zuwa suje wajn Yaya amma kemaimai taki, gobe za'a kawo musu ragowar wasu kayan kamshi na turara jiki wanda na kwana uku ne kachal zaa musu daga nan zaa shiga hidimar bikin wanda bata dauke shi yanzu da muhimmanci ba dan bata san matsayin ta a wajen wanda ake yi domin shi ba. Da safe Amira tazo su tafi wajn Yayan da k'yar sai da Aunty ta bata rai sannan ta amince amma da cewa tayi ba zata ba ta daina zuwa, duk da Amira tasan dalilin amma basu taba maganar ba dan jidda zurfin cikin ta yayi masifar yi mata yawa, ganin bata fada mata ba yasa ta ki mata maganar gaba daya. Ita aka farawa dan Ya Safiyya da Umaima basu ma tashi ba, ana gama mata ta sulale ta koma nasu part din dan tayi alkawarin ba zata yarda su hadu ba. Tana shiga Aunty ta tashi tana rike bakin ta kamshin irin mayatataccen kamshi ne me dadin gaske, kudi sosai aka kashe dan ita kanta daga wani state din tazo matar bayan wacchan ta gama musu ta tafi. "Kinji kamshin da kike Jidda?" Kunya ce ta kamata, ta rufe fuskar ta, da tafin hannun ta tana dariya, kod'a ta Aunty ta dinga yi ita dai kawai dariya take cike da kunyar Auntyn dan abinda ya faru jiya. ***Kwana biyu bayan sun dawo yana ta zuba ido babu ita babu alamar ta, sau wajen uku yana zuwa part din Yaya amma sai ya tarar bata nan, har sai da Yaya ta gaji tace wai lafiya yake mata safa da marwa a gida ne? Fita yayi kawai be sake dawowa ba, chan anjima ya tafi wajn Auntyn amma sai suka hadu da Auntyn a hanya zata fita, ya juya bayan sun gaisa ya samu waje ya zauna yana saka ido ko zai ga fitowar ta amma shiru har dare babu ita babu alamar ta. Be san dalilin da yasa ya damu da son ganin ta ba, shi dai kawai yaji yana so ya ganta ko ma ba zata masa magana ba. Kamar ya koma wajen Auntyn amma sai ya hakura ya fasa. Da safe ya sake saka ido amma shiru, a lokacin ne kuma gidan nasu ya fara cika da mutane, yawanci yan uwan Mama ne suka fara zuwa a ranar, silalewa yayi ya bar gidan dan baya son su ganshi kwata-kwata. ***Suna zazzaune dukka yan matan a falon farko su kuma su Mama na ciki, Salma ce tace tambaye Maryam "Wai Ya Tariq baya nan ne?" "Wa? Ya Tariq din zaki tambayen? Wallahi ban san in da yake ba." "Har yanzu Ya Tariq baya son mutane, wallahi na matsu na ganshi naga yadda ya chanja." "Ganin Ya Tariq sai kin cika Form, da dai Jiddaa ce." Amira tace tana dariya, bata fuska Salma tayi, taja tsaki tana mikewa "Sai ana maganar mutane kuna kawo mana maganar wata chan dan Allah." "Kinyi maganar mijin ta ai dole ayi maganar ta." "Wai miji, tab!" Ta kwashe da dariya "Kina mamaki ne?" "Ba dole ba, dan Allah me ya Tariq zai ci da yarinyar nan? Yarinyar da aka taimakawa aka mayar mutum sai shegen girman kai ita ba yar uban kowa ba." "Aiko baki san jiddah ba." "Bana son ma na santa." "Toh gaskiya ki bar maganar nan kar ma taji wallahi, kinga abinda kika taba yi mata din nan." "Ai ku kome za'a ce akanta bakwa gani, sai kuyi tayi." Turo kofar yayi, ya shigo fuskar sa a tamke,ya dan ji maganganun da suke sama-sama ya kuma fuskanci abinda suke magana akai, shi yasa ya tsani taron mata dan babu yadda za'a yi su hadu su tashi ba su tada fitina ba. Gaishe su sukayi a kusan tare duk sun rude Allah yasa be ji me suke cewa ba, be amsa ba yayi wucewar sa dan dama Mama ce tace yazo ya gaida su Aunty Nafi dasu Aunty Mimi, da ba dan haka ba, da ba zai shigo ba. A tsaitsaye ya gaishe su, ya fito yazo zai wuce Salma tayi tsagal tace "Ya Tariq ina wuni?" Ko kallon in da take be ba, yayi ficewar sa, yana fita su Ummi suka kwashe da dariya, kamar ta kurma ihu haka taji dan kunya. Dama Aunty Nafi ce ta saka ta, tace tayi kokarin shige masa,amma dan wulakanci ko gaisuwar ta be amsa ba bare tasa ran zai kalli in da take. Tsokanar ta suka dinga yi ta rasa ina zata saka kanta sai daki ta gudu saboda borin kunya. ***Shi baki daya baya jin dadin zaman gidan, a matukar takure yake gaba daya da zaman waje dayan gashi ba wani sanin wurare yayi a garin ba dan ma dai yana da saurin gane waje kuma yanzu an cigaba akwai map, gashi Baba yace dole sai ya kara wasu satittikan kafin ya tafi, Mama kuma ta saka shi a gaba tana so taji ya ake ciki, gashi ya rasa yadda zai ko wulgawarta baya gani sau biyu da aunty tana part din Baba yana zuwa ya murda kofar dakin ta amma a rufe zai ji, baya kuma magana yake juyowa dan baya son ta raina shi ko taga kamar ya damu da ita ne, so yake kawai yaga ta daina kukan ko har yanzu tana yi? Gashi ya rasa solution bayan yayi mata alkawari itama, gashi zuciyar sa ta hana shi kemaimai da ya fara tunanin yadda zai yi sai kawai yaga ta fara hasaso masa Jiddan. Wajen Yaya ya nufa duk da itama jama'ar ta sun fara zuwa, wanda dama duk suna burin zuwa Abujan sai kawai Baba yayi amfani da damar nan aka ce duk me son zuwa ya shirya, aikuwa suka dinga tururuwa kafin kace me gidan dame d'am da mutane. Tun a kofar shiga yaji hayaniya sai fasa shiga ya bari idan dare yayi ya dawo. Da daddare Baba ya dawo ya kirashi suka zauna yace menene shirin sa akan tarewar jiddaa, shiru yayi yana nazari har sai da Baban ya sake maimaita masa sannan yace duk yadda akayi yayi, dan jim Baban yayi da zai ce wani abu sai kawai ya fasa "Shikenan, sai ka fara shiri, akwai gidan da zaku zauna, Incase ko baka nan dai muna kusa." "Nagode Baba, Allah ya kara girma." "Amin ya Allah, dan Allah Tariq karka wulakanta min 'ya, Dan Allah." "In sha Allah." "Kuma inaso kuje kai da ita ku gaida mahaifin ta, sai ka saka muku rana bayan sun gama bidi'o'in nasu na mata." "In sha Allah zamuje." "Shikenan Allah yayi muku albarka." "Amin ya Allah." ***Duk yadda Mama taso Tariq ya yi botsare akan maganar auren nan sam yki, ta ma kasa gane in da ya dosa kwata-kwata, kamar ma so yake kawai ta kwantar mata da hankali shiyasa ma yake biye mata da nuna mata shi ma baya son abun. Babu yadda za'a yi baya so kuma ya hakura har a kawo yanzu, wanda nan da kwana biyu zata tare daga nan kuma bata san ya zai yi ba. Yanayin hayaniyar bikin da dumbin mutanen da suka taru yasa ta hakura da maganar ba wai dan ta hakura gaba daya ba, yanzu zatayi focusing kawai akan su Safiyya idan aka gama zata dawo kan Tariq din ne dan ba zata yarda a lalata mata rayuwar dan ta ba. Baki daya gidan idan ka cire bangaren Yaya kowa ya yi shirin tafiya wajen hadaddiyar dinner din da aka shirya, Mama bata nan sun fita da Aunty Mimi daga chan zasu wuce ita da wata babbar kawarta da suka hadu a taron da suke na matan ministoci. Su jidda na wani babban gidan makeup ita da su Ya Safiyya wadda da k'yar akayi convincing dinta ta yarda zaa mata amma yar kad'an dan bata son irin heavy makeup din, ita kadai take budirin ta dan me gayya me aikin kamar ma be san anayi ba, shiyasa Amira zata tsayata su tafi tare driver ya kaisu su kuma Ya Safiyya miijin kowacce ne zaizo su tafi abun su. Su Umaima ne suka fara tafiya sai Ya Safiyya ma ta tafi ya zama sai su kadai dama kuma sune karshen gamawa. Driver Amira ta kira tace sun gama ya matso da mota, yace mata ya dan fita daga cikin wajen zai shigo da Oga yana waje. Yana cewa oga ta gane Ya Tariq yake nufi dan haka yake ce musu shi da Ya Fauwaz dan dama ba bahaushe bane ba. Kin fadawa jiddah tayi sai da ya dawo ya kira sannan tace su taso su tafi. Yana tsaye jikin sabuwar motar sa, wadda Baba ya bashi gift dinta jiya na kammala karatun sa da kuma aure, kaftan ne a jikin sa fari me hade da navy blue collar da jikin hannun, takalmi da hular kansa duk navy blue ne,dinkin da kad'an ya wuce guiwar sa. Kallon wajen yake a tsanake har suka fito, Amira ta hango shi suka nufi wajen da yake a tsaye, sai da suka kusa karasawa sannan Jidda ta ganshi, tsayawa tayi chak cike da mamakin ganin sa, juyowa yayi suka hada ido ya tako ya same su a wajen da suke tsaye "Kije Sam ya ajiye ki,mu ba zamu je dinner din ba." "Ok." Amira tace tayi gaba da sauri, "Muje ko?" Yace yana nuna mata hanya "Tafiya zamuyi da Amira fa." Ta fada idon ta nayi raurau kamar zatayi kuka "Na sani ai, cewa nayi ba zaki je ba, babu wata dinner da zaki oya shiga mota mu wuce gida." "Dan Allah ka barni naje." "Ba zaki ba." "Dan Allah." Ta sake cewa already har ta soma kukan bakin ciki, kukan ka gama saka rai a abu ace ba zaka ba, da tun farko da tace ba zata ba da sun kyale ta shikenan, amma sai da ta hakura har tazo make up sannan yace ba zata ba.. "Oya, muje ko na daga sama, kinsan kuma zan iya." Waigawa tayi ta hango wasu saurayi da budurwa a chan gefen su, ta sake waigawa dayan barin shima wasu ne a zaune suna hira, sai kawai ta nufi motar tana had'a hanyaa. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (32) ***Kofar motar a bud'e take, taje ta shiga ta sunkuyar da kanta k'asa zuciyar ta na tururi, agogon hannun sa ya kalla ya kalli cikin motar, ya kad'a kansa ya tako zuwa wajen motar, ya rufe mata kofar ya zagaya ya shiga ya zauna. "Ki daura seatbelt." Yace yana jan tasa ya daura, ya kunna motar, hawaye ne ya shiga sauko mata na bakin ciki, duk kawayen su na school zasu je Amira ta fada musu Safeera ma zata wuce daga chan dan ta shigo tana gidan aunt dinta. Sake kallon ta yayi yaga bata daura seatbelt din ba, matsowa yayi jikin ta,ta dago ya kalle ta yayi mata murmushi, irin murmushiin na ci karfin ki, kauda kanta tayi ya jawo belt din ya daura mata, ya tsaya daf da ita bayan ya daura matan, k'in juyowa tayi tana jin ji daf da ita, k'ashin wuyan ta ya kalla, yaga rami, hannu ya kai ya taba ta juyo da sauri "Har ajiya za'a iya yi a wuyan nan naki." Yace hannun sa yana kan wajen, fuskar sa a sake yana so ya kure ta, banza tayi masa tana jin yadda yake tafiya da hannun sa akan wuyan nata, wani irin take ji amma ta fuske dan sosai take cikin bacin ran hanatan da yayi wanda bata ga dalili ba. "Kina wannan kamshin turaren zaki shiga wajen da yake da garadan maza? Baki san darajar aure bane?" Yace yana kokarin saka idanun sa acikin nata, "Haramun ne, ki bari mu samu solution sai kiyi ma duk abinda zakiyi, amma dai yanzu na hana,." "Sai ayi sauri a samu solution din, I'm sick and tired, na gaji." Sai ya fashe masa da kuka dan ba karamin haushi maganar sa take bashi ba, kullum sai yayi kokarin shiga rayuwarta haka kullun sai ya jaddada mata jiran lokaci yake, ta gaji kawai ya yanke hukuncin da duk ma zai yanke dama ta riga ta shirya. Tsayawa yayi chak yana kallon ta, kukan take bil hakki da gaskiya, ya rasa kwakkwaran dalilin da zai saka ta dinga irin wannan kukan, be sani ba ko zama kusa dashi ne bata so, ko ganin shi ma gaba daya ne bata so. Gashi shi kuma yana jin shi very comfortable duk sanda suke tare, yanzu ma yana samun labarin zasu dinner ya taho hankalin sa ba a kwance yake ba, baya so taje wajen ayi ta kallon ta, ba kuma dan yana so ko kishin ta ba a nasa tunanin, sai dan kawai ya kare martabar auren sa da yake kanta. "Komai kuka, kuka baya maki wahala ne?" Ya tambaya yana maida kansa ya jingina a jikin kujerar motar yana duban ta, kamshin turaren ta, na fuzgarshi zuwa gareta, sai dai yayi matukar kokarin hana kansa, yana jaddadawa kan nasa cewa . Kokarin daidaita kanta tayi, ta goge fuskar tana hana kukan cigaba da zuwa, kukan bakin cikin abinda yake mata ya kuma nuna sam be san ma me yake ba, yanzu da tayi magana maimakon ya amsa mata sai ma ya tsaya kawai yana kallon ta, ya kuma sauya zancen zuwa wani na daban. Jin tayi shiru ne yasa shi tashi ya sake kunna motar ya ja suka fice daga wajen. Kasancewar babu nisa tsakanin nan da gidan ya saka su saurin isa, hakan ya kara tabbatar mata da ba zata je din ba kenan. Sai da ya shiga har cikin gaban part din Auntyn sannan yayi parking, bata jira komai ba, ta bud'e kofar ta fice, maimakon ta shiga nasu bangaren sai ta chanja hanya zuwa part din Yaya. Parking ya gyara ya bi bayan ta da sauri dan ya hango wasu samari a wajen suna zaune, kasancewar da sauri yake tafiya yasa yayi saurin cimmata, ya rufa mata baya yana kakkareta. Ta ganshi sarai amma tayi kamar bata ganshi ba, suka cigaba da tafiya tana daga kafa yana sauke tasa har suka shiga. Yaya na zaune ita da Gwaggo da wasu a falon ta shigo, ta shige dakin Gwaggon da saurin ta, bude baki Yaya tayi zatayi magana sai gashi ya shigo "A ah, tare kuke ne?" "Eh." Yace yana shigewa ciki shima bayan ya gaishe su a gajarce "Ina wajen bikin kuma?" "Ko har an dawo? Gwaggo tace "A ah be isa an dawo ba, bari naje naji dan yadda Jidda ta shigo kamar ba kalou ba." "Toh Allah yasa lafiya." "Amin." Tace tana mikewa da k'yar dan kafarta ta fara matsa mata sosai. A tsaye ta same shi daga kofar ita kuma jiddaa na saman gadon ta rufe fuskarta, duk kwalliyar da akayi mata ta baci ga shi sai kiran wayarta su Safeera suke Aunty ma ta kirata ta kasa dagawa. "Ya akayi me ya faru?" Yaya tace tana kallon sa "Wai dan nace ba zata je dinner ba, shine take kuka." "Kamar ya ba zata je b? A wanne dalilin yasa ba zata ba?" "Menene amfanin zuwan toh?" "Abinda suka dade ana shiryawa zaka hanata fisabillillah, gaskiya baka kyauta ba wallahi, Jidda tashi kinji, daina kukan haka nan kiyi hakuri, kai kuma sai ka gaya min kwakkwaran dalilin da ya sa ka hanata wallahi, dan ni banga dalili ba." "Ni ba wani dalili, kawai bana so ne, ta bari taje idan babu aure na akanta." "Ahayyye!" Tayi shewa tana tafa hannu, kicin-kicin yayi da fuska Yaya ta rasa me ma zata ce "Ai be kamata ba, tunda dai shi aure daraja ne dashi, kuma ni bana son irin wadannan abubuwan, ta bari a samu hanyar da za'a kawo karshen komai." "Kai tafi chan, wacce hanya ce da ba za'a iya samar da ita ba har sai an ta maganar ta, ai kawai yanke hukunci ake idan har da gaske har zuciya ana neman hanyar, ba a fatar baki ba.". "Tashi kinji Jidda, ki rabu dashi bakin hali ne yayi masa yawa da mugunta, idan ba haka ba a gama shirya abu dan gadara ya hanaki zuwa haba." Tashi tayi idonta har sun daga saboda kukan bakin ciki, gaba Yaya tayi tazo zata raba ta gefen sa ta wuce ya tare hanyar yana mata wani irin kallo da idanun sa suke a shanye, "I'm sorry." Ya samu kansa da furtawa dan da gaske yaji babu dadin abinda yayi mata, kin amsa wa tayi zata wuce ya sake tarewa "Please kiyi hakuri." "Zan rungume ki idan baki hakura ba." Kallon sa tayi da sauri, ya gid'a mata kai, "Da gaske nake Allah." "Na hakura." Tace ganin yana matso ta, amma duk da haka sai da yayi hugging din nata,abinda yake taso tun dazu, yana so ya shaki kamshin jikin nata sosai amma kuma yana hana kansa, daga karshe yaga ba zai iya ba, tunda dai ba wani abu yayi ba, kuma ai ba haramci ya aikata ba. Yaya ce tayi saurin fita dan da ta labe a falon, dariya ma ya bata dan tasan dama wuyar ta yazo hannu, irin su masu sum-sum din nan sun fi kowa iya shege "Almuri." Tace tana zama a in da ta tashi, "Me ya faru Yaya?" "Wai ya hanata zuwa wajen bikin dan shegen kishi." "Abinda kake so ai shi kake kishi Yaya." "Bar dan bantan uba, yana so yana yare, zai gane shayi ruwa ne, dama ai dan hakkin daka raina..." "Haka ne, kina ga a yadda ya shigo fa, kamar ma da fari be lura damu ba." "Ina zai lura so ya rufe masa ido." "Kai Yaya." "Allah kuwa, yaga yar karamar yarinya duk ya rude babban kwabo, da yana cika bakin shi baya so yan-yan-yan." ***A yadda yake ji kamar kafarsa ba zata dauke shi ba, gashi duk yadda taso ya kyale ta, ya kasa, sai da wayar sa dage cikin aljihun gefen rigar sa tayi kara sannan ya saketa yana matsawa baya, da sauri ta koma cikin dakin ta kule chan karshen gefen gadon shi kuma ya d'aga wayar ganin Mama ce "Wai Tariq me kake nufi dani ne?" "Na'am Mama?" "Eh, Jidda bata zo wajn nan ba, sai naji labari na yawo a wajen wai kaje ka dauke ta a gidan makeup kace ba zata ba, me yasa zaka je ka dauke ta? Kuma me yasa zaka hanata zuwa? Bangane maka ba kwata-kwata." _"Ba zan iya bari tazo wajen nan ba."_ yayi maganar kasa kasa amma duk da haka sai da taji shi, "Ba zaka iya bari ba? Saboda kana kishin ta ko?" " Ni? Noo ba haka bane, kawai dai tunda ba wai an riga an rabu bane, dole na kare martabar auren, shine kawai amma ba wani abu bayan nan." "Kasan da yake kai ka haife ni TARIQ, son yarinyar nan kake." "Mama!" "Ka dauka ana wa namiji auren dole ne kuma baya son matar yayi hakuri ya cigaba da bin ta kamar jela, ina lura da kai wallahi, duk take-taken ka na gani." "Amma Mama ba haka bane, ni ba haka bane, ba spec dina bace ba, no ba haka bane gaskiya." "Sai kayi kuma, na bar baki." Ta katse kiran, rike wayar yayi saroro a hannun sa yana jujjuya maganar da Mamsn tayi masa a ransa. Duk maganar da sukayi tana ji kuma ta san akan ta ne, kekashewa taji zuciyar ta, tayi lokaci daya, babu amfanin cigaba da zubar da hawayen ta akan mutumin da ya cika da son kanshi, tasowa tayi tazo har gaban sa, ta tsaya sannan tace. "Kayi sauri ka kawo karshen wannan drama din, kaga sai ka samo daidai da kai din." Daga haka ta wuce shi kawai ta fice daga dakin, ta wuce part din Aunty ta shiga dakinta,tayi kwanciyar ta,tana hana kanta sake kuka akan sa. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (34) ***Wajen Yaya ta nufa dan tasan itace kai tsaye zata saka Baba ko ta hanashi. Ta kuma san ta yadda zata bullo mata ta daina ragawa Mama dan ta lura shirun ta yasa take ganin har yanzu tana da ikon taka ta. Bedroom din Yayan ta shiga ta sameta a kwance tana hutawa bayan ta idar da sallar walaha, tashi tayi zaune suka gaisa sannan tace magana tazo su yi "Ina jinki Halima, mecece matsalar? Dan nasan dole akwai magana." "Yaya dama akan maganar Jidda ce, ni a gani na tunda har Tariq ya dawo Jidda ya kamata ta tare a gidanta, dama taron bikin ake so ayi kuma ya nuna baya ra'ayi ni a ganina kawai ta tare shine mafi a'ala." "Ni kaina nayi wannan tunanin kuma jiran Alhaji nake ya shigo, dan na ga alama dan ku bashi da ta ido sam, gwara su je chan su karata." Dariya ta saka Yayan ta cigaba da bayani "Al'muri da yake munafuki ne ai kinga yadda yake ko? Irin masu halin nan ke dai kawai ki kalle su, sun fi kowa iya shakiyanci." "Yanzu ki barmun komai, a yau ba sai gobe ba zata tare, dan babu amfanin zaman." "Allah ya kaimu Yaya, dama dai maganar kenan abun ya soma damuna." "Ai dole, yarinya ma tayi hakuri ki bari zanyi maganin shi a yau din nan, sai kisa ta shirya duk abinda zatayi zuwa anjima." "Toh bari naje Yaya, Allah ya kara girma." "Amin kinji? Allah yayi albarka." ***Komawa tayi ta saka jiddah a gaba, da Safeera da ita suka taimaka mata ta hade koman ta waje daya, hannu bata saka ba ita a lallai ba in da zata tunda be san worth din ta ba, babu wadda tabi ta kanta musamman Safeera da tasan munafurci ne kawai ba har zuciyar, take maganar ba. Falo ta dawo tayi zaman ta, tana kissisima yadda zata kaya a zaman nasu, duk da kaso hamsin tana tsoron Mama amma kuma sauran kason na kwadaituwa da son zama dashi din. Fitowa Safeera tayi ta sameta a falon suka cigaba da zama sai ga Isma'il ya kirata, dagawa tayi jidda tayi kamar bata gane da wanda suke waya ba, suka dan jima suna magana daga karshe ta kashe tana murmushi "Ya Isma'il ne, kinsan ya kusa zuwa gida." "Allah sarki, Allah ya taimaka." "Amin, ni tunda tafiya zakiyi ma ai ba amfanin zama na, zan koma gidan Aunty Sajida kawai." "Wai waye yace miki tafiya zan? Ki jira mana ki gani, nasan ba in da zanje." "Toh zamu gani, yarinya gwara ma ki saka ranki tafiya dole." "Idan nace ba zani ba ai babu me daukata. " "Wallahi tsaf zai dauke ki din, tab!" "Ke kika sani." "Ke ma kin sani ai." ***Ran Mama ya kai karshe a baci, dawowar ta kenan daga wajen Yaaya da ta turo aka kirata ta fada mata yau matar Tariq zata tare, da k'yar ta amsa da toh ta taso tazo ta fadawa su Aunty Nafi, suka kuwa hau fanfata akan karta yarda. Kiran TARIQ tayi be daga ba, sai ta kira Fauwaz shima sai da ta katse sannan ya biyo kiran tace masa ina Tariq yazo maza-maza, baya nan dan tun safe da ya fita training be dawo gidan ba, gidan sa ya wuce a chan yayi wanka ya shirya sannan ya koma bacci dan yasan idan be more baccin sa ba ya koma sai ya samu matsala, shiyasa har Maman ta kira be ji ba. Sai da rana tayi sannan ya tashi ya dan sake gyara jikin sa sannan ya hau mota ya dawo gidan. Tun a hanya dama Fauwaz ya fada masa Mama tana neman sa, shiyasa yana zuwa part dinta ya wuce tana ganin sa tace ya shigo suka shige chan dakin ta in da babu kowa. "So nake ka saki Jidda a yanzu ba sai anjima ba." Kawai tace masa ko zama bata iya yi ba. Kallon ta yake hankalin sa a tashe, ta hade rai taki bari ko kad'an yaga saukin ta, kasa furta komai yayi, ya dinga kokarin tattaro kalaman bakin sa amma ya gaza furta su, idan har yace zai iya sakin Jidda yayi karya, duk da ba wai yana mata son da ba zai iya rabuwa da ita ba, amma ba zai zo ya samu matsala da iyayen sa akan ta ba, haka kuma ba zai taba so hakan ta shafi iyayen sa ba "Mama dan Allah mu bari mubi komai a sannu, dan Allah " "Babu wani bin komai a sannu, yau kwana nawa kaana min alkawari amma ka gaza cikawa sai bin yar karamar yarinya a baya kamar wanda aka gama dashi." "Wai Maama waye yace bin ta nake?" "Kasan ni yarinya ce ai, bansan me nake ba." "Ba haka bane Mama." "Toh naji, duk ba wannan ba, bana son zaman ku karkashin inuwa daya, dan haka sai ka sawaake mata tunda ka kasa samun mafita." "Baba fa? Zai yi fushi dani sosai." "Ka barni dashi kawai, kai dai kayi abinda nace, ba zan iya jure ganin ta a matsayin sirikata ba." "Amma Mama, mesa kika tsaneta haka?" "Tambaya ta kake?" " A'ah, kawai dai naga kamar yayi yawa ne mama, kiyi hakuri dan Allah mubi komai a sannu, Dan Allah muyi wa Baba biyayya kar muzo muyi abinda zai bata masa suna shi yanzu da yake a idon duniya abu karami zaki ji ana yi dashi." "Ba zan ba, akan yarinyar nan zan iya batawa da kowa, idan har jinin Halima ce zata auri jini na, na gwammace komai ya faru." "Mah?" "Idan har na isa da kai, ka rabu da ita." "Menene laifin ta a gareki Mama?" "Babu komai, ba abinda tayi min kawai bana son ta ne." "Shikenan mama, zanyi abinda kike so, amma ina zuwa Dan Allah." Fuskarta ce ta fadada da farin ciki, t "Dan Allah da gaske kake?" Daga mata kai yayi "Toh madallah, ka gama min komai Allah yayi maka albarka." "Amin Ya Allah." Ya juya ya fita ita kuma ta koma wajen su Aunty Nafi zuciyar ta cike da farin cikin zata kuntata wa Auntyn dan dama tayi alwashin sai ta mata abinda zata dade tana jin ciwon sa. Ko da ya fita sai ya rasa abinda yake masa dadi, ko giyar wake yasha ba zai iya aikata abinda Maman take so ba, dan ba itace akan gaskiya ba, Baba yafi ta gaskiya dan haka dole ne yasan yadda zai yi be bata wa daya daga cikin su ba. Iyaye dole ne ka bisu kayi musu biyayya kuma mahalifiya tafi karfin wasa shiyasa yake matukar yi mata biyayya domin samun rabauta. Amma kuma a wannan gabar be san me yasa ba, baya jin yana tare da Maman. Zaman sa yayi a waje tare da masu gadin gidan lokaci zuwa lokaci yana dan saka musu baki a hirar dan yadda gidan yake cike da mutane bazai sake shiga ciki ba, tunda dai hankalin Maman ya kwanta for now zai tafi da ita a haka kafin yasan abun yi. Sai da akayi la'asar sannan ya tashi daga wajen, ya shiga cikin dakin su ya hau tattare muhimman takardun sa waje daya, ya zuba su a yar karamar jaka ya saka a bayan mota, sannan ya tafi kiran Yayan da ta turo tana neman sa. Chan cikin dakin ta, ta kule dan ba kowa take so yasan maganar da zasuyi ba. Mamakin ganin ta a nutse a zaune yasa shi shan jinin jikin sa "Lafiya Yay?" "Lafiya ta kalou wallahi." "Menene ya faru?" "Takardr jidda zaka ban?" "Takarda kuma Yaya?" "Eh, tunda baka son ta ba, ka sakar musu 'ya taje ta auri wanda yake son ta." "Wanene?" Ya bata fuska "Ina ruwan ka? Wani ne yazo tun kafin ma ayi maganar ka, wai mu masu shishigi da son gwaninta muka ce gida be koshi ba,ashe zaka zo ka watsa mana ido?" "Aina yake shi din?" "Oho ba zaka ji ba, ka bata takardar ta ba sai ta sake kwana da igiyoyin auren ka akanta ba." "Kuma ita ma tana son shi?" "Kaji mun yaro, ina ruwanka da wannan kuma? Kai tunda ba da gaske kake ba, ai sai kawai ka yanke hukunci Amma ba zai yiwu ka hanata kula kowa ba kai kuma baka so." Mikewa yayi ransa a baci ya fice be sake cewa komai ba, dariya suka kwashe da ita, Fauwaz dake makale ya fito suka tafa da Yaya "Kinsan ta kan tsiya Yaya." "Ni din ta wasa ce? Sai shegen kishi amma girman kai ya hana shi gane halin da yake ciki." "Ya sani fa Yaya, kawai yana hana kansa yarda da hakan ne, bari muga abinda zai yi kuma, bari naje naji yadda ake ciki." "Karka manta kazo ka fesa min." "Akwai amaana ai ni dake tawan." "Amanar kad'an ce, tunda ka kusa kashe ni na dawo daga rakiyar ka, bakin mugu." "Ai ya wuce sai zamu Kano sallah, da kafarki zaki taka ki shiga jirgin ma Hajiya Yaya." "Bana so, babu kuma shegen da zai saka ni shiga." "Zamu gani dai, bari naje nagano." "Munafuki." Tace tana kallon sa, be ji me tace ba, ya fice dan da yaji sai ya dawo sun yi ta da ita. Kai tsaye part din Aunty Tariq ya nufa ransa a bace fuskar nan tasa a hade tamau, babu kowa a part din Aunty na side din Baba, ita kadai ce sai Usman da yake wasa a falo yana kallon Disney World, tasowa yayi da sauri yayi hugging din Tariq din, ya d'aga shi sama yana kokarin daidaita fuskar sa "Wasa kake?" Yace yana sauke shi k'asa "Eh tare muke yi da Yaya Jidda tace zatayi sallah." "Ina Aunty?" "Ta fita." "Ok zauna kayi wasanka ko? Ina zuwa." Yace ya nufi dakin Jiddan, ta idar da sallah kenan taji rigar dake jikin ta, ta takura mata, sai kawai tayi deciding ta cire ta, data raka Safeera ne ta sakata amma dama bata iya zaman gida da ita, riga da wandon ta ciro na bacci masu dan kauri rigar iya guiwa sai dogon wando, ta saka tana gyara gashin kanta da ya barbazu akan nata ya murd'a kofar ya shiga da sallama muryar sa a chunkushe kamar wanda ya saka wani abu a makoshin sa ya tokare wajen. Kasa dagowa tayi tayi tsam a wajen da take ya shiga takowa yana karewa dogon gashin nata kallo. A daf da ita ya tsaya ta kalli kafarsa dake sanye da takalmi sau ciki. Muryar tasa a ciki-ciki yayi magana "Ina Hijab dinki?" Bata amsa ba, dan bata ga amfanin tambayar ba, wurwurga idanun sa yayi tayi a cikin dakin ya taka zuwa wajen da kayan ta suke, ya bude wardrobe din yana kallon jerin kayan dake gyare a cikin wardrobe din. "Lefe." Ya fado masa a ransa, hannu ya sa ya ciro Hijab guda daya a cikin jerin kayan, pant dinta ne ya fado, ya sunkuya ya dauka ya kalli wajen da take a tsaye, da sauri ta kautar da kanta kunya matsananciya na kamata, ciki ya mayar ya rufe ya dawo ya mika mata, sannan ya dauki wayar ta dake ajiye a saman gadon, yace tasa Hijab din. "Ina zamu?" Tace rike da Hijab din bata saka ba "Gidan Mijinki zaki." Ya amsa mata kai tsaye, yayi hanyar barin dakin sai da ya kai karshe sannan yace "Karki bata min lokaci." [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (33) Be iya motsawa daga wajen ba, maganganun Mama da nata na cigaba da yi masa yawo akai, toh ko dai son nata yake? Ya tambayi kansa. No ba haka bane. Wata zuciyar ta rad'a masa, tausayin ta kawai kake ji, ya sake jin wata zuciyar ta tunasar dashi. "Eh haka ne, tausayi ne kawai nothing more." Yayi assuring kansa yana samun hujjar da zai rike, kad'a kansa yayi ya fito daga dakin, duk da maganar ta, ta bata masa rai amma kuma ba zai yi abinda suke so ita da Maman ba, sai yayi istikara sannan ya samu gamsashishiyar hujjar da zai rikewa Baba ya yarda dashi. Wani kallo Yaya tayi masa da ya fito, yayi kamar be ganta ba yayi ficewar sa, ta yi dariya tana girgiza kanta, tasan akwai sauran drama amma kuma a chan k'asan zuciyar tana tausayin Tariq din, dan tasan irin su so be iya yi musu da dadi ba. Tunda ta shiga dakin take juyi a gado, kamar ta tattara kayan ta, ta tafi wajn Baffa haka take ji, baki daya babu abinda yake mata dadi, tana nan kwance har aka soma dawowa, su aunty ne yan farkon tahowa suka taho tare da Safeera da zata kwana a gidan. Tana jin su ta fito da sauri, suka rungume ita da Safeera idon Aunty akanta, sai da suka zauna sannan Auntyn tace "Jidda me ya faru ne wai?" Turo baki tayi cikin yanayin rashin jin dadi tace "Hanani yayi." "Tariq hoo, amma me yasa?" "Nima ban sani masa ba, kawai mugunta ce wallahi." Tace kwala na sake taruwa a idon ta dan ko tunawa tayi sai taji hawaye "Karki kara cewa mugunta duk tsiya mijinki ne, kuma duk abinda yace shi zakiyi." "Aunty amma kinsan be kyauta ba ko?" "Toh me zan ce jidda, tunda shine yake da ikon barki ko hanaki." "Aikuwa, kuma dole ayi biyayya." Safeera tace tana dariya, duka Jidda takai mata, tace ta taso su shiga ciki, suka bar Aunty ita kadai sai itama kawai ta wuce dakin ta dan watsa ruwa ta dan warware gajiya.   Bayan tayi wankan tana zaune a falon akayi knocking, kasancewar duk masu aikin gidan idan dare yayi basa shigowa suna bq yasa ba kowa sai ita kadai a falon, tashi tayi ta bud'e kofar sai taga Tariq a tsaye, matsa masa tayi ya shigo sannan ya rufe kofar "Aunty yunwa." Yace yana zama idon sa akan hanyar dakin Jidda "Bari naga ko zaka samu wani abun a kitchen." "Aunty Indomie nake so, tunda nazo banci ba, a kira sai ta dafa min karki wahalar da kanki." "Aikuwa Jidda gwana ce, dan tafi ni ma, suna ciki da kawarta Safeera bari na kira ta." "Nagode Aunty." "Ah ba komai ai, bari na turo ta." Tayi gaba tana murmushi, a kalla yanzu ta tabbatar da Tariq yana son Jiddan ta, abinda dama yake daga mata hankali kenan, sai gashi duk kowa ya gama gano shi duk da shi be gama gano kansa ba, he's so obsessed with her. Knocking tayi musu daga kofar ta dan bud'e tace "Zo ki dafawa Tariq Indomie yunwa yake ji." Zaro ido tayi, "A daren nan Aunty?" "Eh yana falo yana jiran ki, ni kwanciya ma zan dan na gaji sosai, sai da safe Safeera." "Sai da safe aunty." "Jiran ki yake." Ta maimaita mata ganin tana zaune ko motsi batayi ba, tashi tayi ta dauko Hijab ta zunbula har k'asa sannan ta zura slippers ta fito tana zumburo baki Safeera na mata dariya, "Idan naji kin dade zan rufe kofa ta " tace mata tana dariya "Allah ya kiyaye na dade, sama-sama zan dafa masa na dawo daki, a daren nan ace ka wani dafa abinci kawai dan a kuntata maka." Tayi maganar bayan ta rufo dakin yadda Safeeran ba zata jiyo ta ba, yana tsaye jikin bangon corridor din duk yaji me tace, kallon sa tayi gaban ta, ya fadi, ya kad'a kansa yana nuna mata hanya "Wuce na fasa Indomie din ma, sakwara nake so." "Wallahi ban iya ba." Tace da saurin ta, dariya taso bashi ya kanne yana nuna mata hanya "Ita mijinki yake so dole kuma ki yi masa abinda yake so ko na fadawa Aunty." Tafiya ta cigaba da yi zuwa kitchen din ya take mata baya, ya samu jikin freezer ya tsaya yana folding din hannun sa, tsayawa tayi tana kalle-kalle kamar me neman wani abu, "Dafa indomie din amma kikayi min sama-sama sai kin daka min sakwara da tiny hands din nan naki." Indomie din ta dauko ta, ta dora yana kallon ta, "Bana son jagwalgwalo kuma." "Ni bana iya abu idan aka sakani a gaba." "In fita kenan?" "Eh." Tsalle yayi ya haye saman deep freezer din "Karewarta ma kenan, kiyi sauri kuma karki sa yunwa ta kama ni." Bata sake magana ba, ta cigaba da abinda take yana kallon ta, waya ya ciro ya hau dannawa ta juyo kad'an taga hankalin sa na kan wayar, yaji ta dauko ta kara a Indomie din ta rufe duk be gani ba. Ta gama ta saka masa chicken a ciki amma sai yace ta soya masa egg, nan ma kamar ba zatayi ba ta soya egg din ta hada komai a tray amma sai yace mata saura oat, kamar tace ba zata dama ba amma dai ta daure dan ta lura shi kamar zaman shi a kitchen din be dame shi ba. Dining ta wuce ta dora akai bayan ta gama, ya duro yana maida wayar aljihun sa, ya tako zuwa wajen dining din, yaja mata kujera daidai in da ta ajiye abincin "Zauna." Yace yana rike mata kujerar. "Na'am?" "Sit down!" Zama tayi ya tura ta ya maida kujerar jiki yana tsaye daga bayan ta "Oya, cinye tatas." "Bana jin yunwa." "Wallahi sai kinci, ina kallo kika zuba mun yaji ai, so kike na mutu ko?" Ya zuro mata kansa ta bayan kujerar "Ai me yaji tafi dadi." "Oya, ci." Daukar fork din tayi ta fara ci, wani masifaffen yaji ya shiga har cikin kwanyar kanta, bata son yaji komai kankantar sa, shishi ta fara ya yi murmushi yana cije kasan lips dinsa, "Yaji ko?" "A ah kwarewa nayi." "Ok sannu, oya eat maza-maza." Jujjuya fork din ta soma yi, ya ja kujerar gefen ta, ya zauna yana tallafe fuskar sa. Narai-narai tayi da fuska kamar zatayi kuka amma ya fuske, ya dauki oat din ya fara sha, yana kallon ta. "Dan Allah kayi hakuri ba zan kara ba." "Me kikayi?" "Yaji na saka maka." "Me yasa?" Ya tsare ta da idanun sa, sauke kanta tayi kasa da sauri "Oya tell me, me yasa kika cika min yaji?" "Nima bansani ba." "Toh karki sake." "Ba zan sake ba." "Good girl, kije ki kwanta toh, sweet dreams" Da sauri ta mike, dama jiran kad'an take, tayi gaba ya bita da kallo ya girgiza kansa, yayi sauri ya karasa shan oath din ya tashi ya bar part din. ***Washegari da safe Aunty na dakin ta, Rasheeda tazo ta sameta wai Mama na falo tana magana da ita, abin ne ya bata mamaki dan tunda ta dawo Abujan sau daya Maaman ta shigo shashen ta shima rashin lafiya tayi har da karin ruwa shine tazo a tsaitsaye ta duba ta. Tasowa tayi cike da mamaki ta fito sai ta sameta a zaune tana karewa falon kallo, tana ganin Auntyn ta fito ta mike tsaye "Ina kwana Maaman Fauwaz?" "Lafiya, ina Jidda?" "Jidda kuma? Me ya faru?" "Bani da damar kiran Jidda kenan?" "A ah ba haka bane, bari na kira ta." Tace, girgiza kafa Maman tayi bayan ta koma ta zauna wajen da ta tashi, zuwa tayi ta kira Jidda, suka fito tare. Ganin Maman a zaune yasa ta samu k'asa ta zauna ta gaishe ta cike da girmamawa, amma maimakon ta amsa sai ta shiga aiwatar da abinda ya kawo ta "Me kikayi wa Tariq?" "Na'am?" "Me kikayi masa? Wanne kalar asirin akayi ma d'ana da har ake so ya zama wani sulobiyo yana bin ki kamar wani jela?" "Kamar ya wai?" Aunty tace "Kamar yadda kuka sani,nasan idan har ba wani abun kukayi masa ba wallahi Tariq yafi karfin ya dinga bibiyar ta haaka." "Haba Maman Fauwaz, mu babu abinda mukayi masa wallahi, me zamuyi ma? "Oho, wallahi ba zan dauka ba, ba zai yiwu a maida min yaro wani gashi nan ba, tun wuri ki sani wallahi, dan wannan karon da karfi na nake, kuma zan yi komai na karya wannan kaddararren auren." Sai ta mike, "Ki shirya bugawa dani a wannan karon, dan bana hada Tariq da kowa saboda haka ba zan taba bari ba wallahi." Sai ta juya ta fice kamar kububuwa, dariya Aunty tayi bayan ta fice jiddah da ta tsorata ta kalli Auntyn "Share ta Jidda, wallahi ba abinda zata iya duk barazana ce, kuma idan ta isa sai ta hana Tariq din ko? Amma ba ke zata zo tana fadawa magana ba,na daina yi mata shiru wallahi, duk abinda tazo dashi a shirya nake nima, Tariq kuma in sha Allah sai kin haifa masa yayan da zata goya a bayan ta." "Aunty ni tsoro nake ji, dan Allah ko a hakura." "Akan me? Wallahi ba a isa ba, ki zauna shekara guda kina jiran sa ya dawo sai ace a hakura? Saboda mu ne bamu da galihu ko? Toh ba'a isa ba wallahi, kuma a yau ba sai gobe ba, zaki tattara ki tafi gidan ki ai an gama komai, ban ga zaman me kike ba ma." "Bari kiga." Tace ta dauki veil dinta ta rufa kanta ta fita, tashi Jidda tayi ta koma dakin ta duk babu dadi, bata son tashin hankali kuma bata so Aunty ta yi abinda da batayi ba akanta. *_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_* _(Where every flavour tells a story .....)_ *_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_ _08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_ _INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*? GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_ _MU NA YIN:_ *_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_* *_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_* *_LOCAL DRINKS:_* _HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_ _MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._ _KADA KU MANTA MUNA YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._ _FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_ _ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_ _PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_ [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (36) *** "Na shiga uku." Tace tana jin kamar k'asa ta bud'e ta shige ciki, "Fada min ina so na sai wasu kaya ne." Turo bakin ta tayi gaba, ta wuce taja kujerar mirror ta zauna, murmushi yayi ganin dabi'ar tace turo bakin,ya kuma san maganin ta, cigaba da duba kayan yayi ya zabi dogayen riguna da kiyasin tsayin ta da nasa amma dan ya sake tabbatar wa sai ya janye system din ya mike ya nufi in da take a zaune ya saka hannu biyu ya mikar da ita, sannan ya karata a jikin sa, yar karama take tashi a duk sanda suka tsaya a tare, saboda shi yana da tsayi sosai. "Menene tsayin doguwar rigar ki?" "54." Tace tana kauda kai ganin kamar leken wuyan rigarta yake yi wadda take v-shape, duk a takure take "Ashe daidai nayi guessing, nasan ba zaki fi hakan ba, little Jiddah." "Little?" "Yes." Ya d'age mata gira, "Zo kiga wani abu." Yaja hannun ta, ta kalle shi da sauri shima ya kalle ta saboda yadda sukayi wa juna shocking "Like charges repel, unlike charges attract." "Na'am?" "Haka akace a physics." "I'm not a science student." "I see, amma zaki iya fadamin?" "Me?" Tace tana daga kanta ta kalle shi, shiru yayi kamar ba zai magana ba, sai kuma yace bayan ya rike mata hannun kakam "Size of your underwears." "Wayyo Allah na, Dan Allah ka daina." "I need to know, ina siyan kayan lefe ne." "Lefe?" "Yes, ba ana lefe ba idan za'a yi aure ba." "Aure zakayi?" Ta samu kanta da tambayar sa, gid'a mata kai yayi "Aure zan, shiyasa zan hada lefe kuma ke zaki tayani zaba." "I can't." Ta janye hannun ta fuskar ta na chanjawa nan da nan, kallon ta yake yana karatar yanayin ta,ya kuma hanata kwace hannun nata, shafa kansa yayi da hannu daya yayi murmushi yace "Muje ki fara zabar min masu kyau kuma kar amarya tace ban iya zabe ba." Wajen da ya ajiye system din ya jata, ta haye gadon ya zauna a gefen ta yana saka system din a tsakanin su, ya shiga nuna mata kayan tana kallo, duk wanda ya nuno sai tace be kyau ba, har suka dau lokaci a haka ba tare da ta zabi kowanne ba, sunan Yasmin ne kawai yake mata yawo aka, tasan ta gama haduwa iya haduwa dan tasan Tariq bazai kula yarinya kamar ta ba. Zamewa tayi ta kwanta bayan ta dan matsa zuwa dayan side din gadon, ta rufe idon ta taja duvet ta rufe har kusan kanta. Tattare system din yayi da wayoyin su ya dora a saman chest of drawers, ya karo sanyin dakin ya kashe wutar ya hawo gadon ya kwanta a wajen da ya tashi, ya bar space a tsakanin su. Juye-juye suka dinga yi dukkan su, kowa da abinda yake sakawa a ransa "Little Jidda?" Ya kira sunan ta yana matsawa zuwa tsakiyar gadon,amsawa tayi ciki-ciki, ya saka hannu ya juyo ta suka kalli juna ta dan hasken da ya shigo ta corridor din dakin "Tell me about you, everything about you kinji?" Dan motsawa tayi ya sake jawota sosai zuwa jikin sa, "Fada min, bani labarin Jidda." "Yanzu? Bacci nake ji fa." "Ba wani, inajinki kina ta juyi, kin kasa baccin." "Ni da gaske bacci nake ji har na fara ma." "Oh okh, to bari na saka ki wartsake." Sai ya matso da fuskarsa wajen tata, ya rufe idon sa ya hade bakin su waje daya. Kamar yadda ruwa yake idan ya dauke haka tunanin jidda ya dauke, ya kwasheta ya sauke ta a wani bigire na daban, kasa ko da kwakkwaran motsi tayi, tana jin shi cike da mamakin sa, sai da ya gaji dan kansa, sannan ya matsa da kansa baya ya dora shi a saman pillow yana kallon saman daki, _"Me ya same ni ne?"_ Ya tambayi kansa. _"Me yasa nake kasa controling kaina when I'm with her?"_ Ya sake tambayar kansa. Tana da wani irin tasiri akansa, a kanta yake bude baki yayi magana sosai fiye da yadda take yi masa kuma shima yake yiwa kowa, baya tunanin komai da kowa a duk lokacin da take gabanta. Murmushi yayi yana jin taste din salivar dinta a cikin bakin sa, dama he has been longing for this , ya dade yana imagining kansa kissing her small lips, he never expected her to be this sweet, a dah kallon karamar yarinya yake mata wadda yake ganin ba zata iya masa ba, kuma ba zata iya da needs nashi ba, but ya fara proving kansa wrong, and he is developing feelings for her, duk da babu yawa amma kuma yasan ko yaya ne dai. Juyowa yayi da kansa yaga ta sake juyawa dayan side din, yasan kunya taji, sai ya kyale ta kawai ya juya ya rufe idon sa, ko minti biyar be kara ba bacci yayi awun gaba dashi. ***Da asubah ta riga shi tashi, ta kalle shi babu ko riga a jikin sa sai 3quater wando, duk kuwa da sanyin dakin, ta rasa dalilin da yasa ko sanyin baya ji bayan ita har hancin ta ya toshe saboda sanyi ya kure AC kuma ya cire riga, shi jin zafin nasa ma extraordinary ne, toilet taje tayi alwala ta fito ta sameshi ya tashi ya kunna hasken dakin,alwalar da tayi yasa sanyin da take ji ya karu, yazo ya wuce ta ya shiga toilet din shima, rage sanyin tayi sosai ta kudundune da blanket sai da taji sanyin ya dan ragu sannan ta tashi ta dauko Hijab din ta saka ta shinfid'a sallaya zata tada ikama ya fito da ruwa a jikin sa yana gogewa da towel alamun wanka yayi, jallabiyar ya dauka ya saka ya ciro hula irin wadda ake kira da tashi ka fiya naci fara ya dora akansa ya fice da sauri dan kar ya rasa jam'i. Tana nan akan sallayar ya shigo dakin da sallama, ta amsa kanta na kasa bacci na fizgarta, zuwa yayi ya duka a gabanta ta dago jin shi a kusa da ita "Baki bacci ba?" Ya kalli idon ta, da suka dan tasa, girgiza masa kai tayi "Nayi." "Ok, yau daurin auren yaran chan, munyi waya da Baba yanzu da wuri zan fita,dan Kano zamu a sumaila za'a daura auren ki kwanta kiyi bacci kinji?" Ware idon ta, tayi da sauri taji ta nemi baccin ta rasa "Ni ba zan je ba? Ba zani gidan ba?" "Eh." Yace mata kai tsaye "Ni kadai zan zauna?" "Eh." Yace mata nan ma "Dan Allah kayi hakuri, wallahi tsoro nake ji, kuma duk su Amira suna nan har kayan da zamu saka yau an karbo, dan Allah ka barni dan Allah." Sai ta fashe masa da kuka wiwi, yana durkushe akan digadigin sa,yana kallon ikon ALLAH, abu kad'an sai kuka? Me zata je tayi toh kuma? Baya son duk abinda zai faru tsakanin shi da Mama ya shafe ta, yasan nata sai yafi zafi shiyasa yaga gwara tayi zaman ta. "I'm sorry kinji, zan turo su Amiran sai su zauna dake." "Ba zuwa zasuyi ba, biki ake fa." "Toh shikenan, babu abinda zai sameki ai,akwai masu aiki a waje, Fauwaz zai kawo duk abinda babu a kitchen." Sai ya mike ya isa wajen kayan sa, ya dauko sabuwar shaddar sa fara kal da babbar riga, ya dauki takalmi, agogo da hular sa, da sauran abinda zai bukata, dan a gidan zai shirya, mota yaje ya kai ya dawo har lokacin kukan take sosai, baya so ta karyar masa da zuciya har yace taje, sai kawai ya tsaya daga kofar yace mata ya tafi, ko dagowa batayi ba, yayi jim a tsaye sai kuma ya juya ya fita dan baya so Baba ya kuma kiran sa dan babban aiki ya sashi, kuma sune zasuyi gaba kafin su Baban su iso shiyasa ma ko breakfast be tsaya yayi ba. _RANO SCRUMPTIOUS MEAL_* _(Where every flavour tells a story .....)_ *_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_ _08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_ _INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*?  GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_ _MU NA YIN:_ *_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_* *_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_* *_LOCAL DRINKS:_* _HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_ _MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._ _KADA KU MANTA MUNA  YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._ _FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_ _ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_ _PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_ [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (35) ***Kasa daga kafarta tayi daga in da take tsaye, taji kamar ana sassara mata su, tsoro ne ya shige ta, tsoron abinda zata tarar idan har ta bishi, bata yi tunanin da gaske aunty take ba,da tace yau zata tafi, sai ta dauka kawai tsokanar ta sukeyi, a yanayin da ya shigo mata ta tabbatar ba da wasa yake ba, me ya kamata tayi? Ta tambayi kanta tana tsaye rike da Hijab din gashin kanta a barbaje dan ko ribbon bata saka masa ba. "Aunty." Tace tana kallon in da ta ajiye wayar ta da nufin ta kirata a waya tazo tunda tana part din Baba. Babu wayar a wajen, dudubata ta shiga yi amma bata ganta ba, tasan kuma a saman gadon ta ajiye ta, cigaba da dubawa tayi tana rike da Hijab din tana tunanin abinda ya kamata tayi.    In da yasan zai samu Auntyn ya nufa, yayi knocking a kofar ya tsaya rataye da hannayen sa a bayan sa. Bude kofar tayi, "Tariq?" "Aunty zamu tafi ne dama, shine nace bari na fada miki." Wani irin sanyi taji a k'asan ranta, tayi murmushi tana gid'a masa kai "Ba komai ai, akwai kayanta a wata trolly sauran sai a kawo mata da safe, Allah ya tsare ya taimaka." "Amin , Baba be dawo ba?" "Yana hanya, zamuyi magana dashi." "Nagode Allah ya kara girma." "Amin Amin." Tace ta kasa boye farin cikin ta, wucewa yayi sai da ta daina hango shi sannan ta rufe kofar zuciyar ta cike da farin cikin Jidda zata samu nutsuwa da sauyin rayuwa irin wadda take mata fata. Tana tsaye ta gama dube-duben wayar bata ganta ba sai gashi ya shigo, be kalli in da take ba, ya saka hannu yaja akwatin yayi gaba. Yanayin fuskar sa kadai ta ishe ta ta gane ba da wasa yake ba, dole ta saka Hijab din ta tura ribbon din a hand bag dinta tabi bayan sa a sanyaye.   Har ya shiga mota tunda a gaban wajen yayi parking dinta dama, ta hasken da ya haska cikin motar ta hango shi yana kokarin tada motar, kofar gaban a bud'e take, ta karaso ta shiga a sanyaye ya yi reverse suka fita daga gidan. Babu wanda yayi ko tari a cikin su, tukin sa kawai yake har suka isa gidan dake dauke da me masu gadi da securities saboda yadda rayuwar ta zama yanzu. Gida ne madaidaci wanda be cika girma sosai ba, amma kuma ya yi kyau sosai ya dace da masu gidan. Idanun ta akan compound din gidan sanda yayi parking a gefen wata mota dake fake a cikin gidan baka me kyau. Kashe motar yayi ya fita, itama sai ta fito duk da be ce mata ta fito din ba, ya mikawa wani matashi car key din sannan suka haura saman balcony zuwa kofar da zata sadaka da cikin gida. Yana gaba tana bin shi a baya suka shiga cikin falon da yake a matukar tsare, ko ina fes fes komai na ciki sabo ne kal an kawata falon da kaya kalar golden masu daukar ido.   Hular dake kan sa ya cire ya ajiye a saman centre table din dake tsakiyar falon ya wuce zuwa bedroom din da ya maida shi nasa, dan tuni duk ya tattaro kayan shi daga gida ya kawo su. Cire kayan da yake jikin sa yayi ya sauya zuwa doguwar sakakkiyar jallabiya milk colour ya fesa turare a jikin sa. Ya zauna yana ciro wayar sa da tata, ya bud'e ya saka number sa ya kira yaga tata number din yayi saving sannan ya jona su a jikin chargy ya kwanta a kan sofa yana mike kafarsa. Be san ko hukuncin da ya yanke yayi daidai ba, shi dai kawai yabi abinda zuciyar sa ta fada masa ne.    Kiran wayar sa akayi, ya tashi yaje ya dauko sai yaga Baba ne yake kira, nauyin Baban yake ji a yanzu dan be san yayi abin kunya ba sai da yaga kiran Baban. Kamar ba zai daga ba ganin zata katse yasa ya daga. "Baba barka da dare." Yace yana kokarin danne kunyar da yake ji "Barka dai Tariq, ashe kuma kun wuce sai da na dawo nake samun labari." "Na'am..." Yace yana sosa kai, dariya Baba yayi "Shikenan ka shigo da safe inason ganin ka, kar kuma ka manta da maganar da mukayi akan zuwa gaida Baffan naku." "In sha Allah ba zan manta ba." "Toh madallah, Allah yayi muku albarka." "Amin ya Allah, sai da safe." "Mu kwana lafiya ango." Baba yace cikin sigar tsokana, ai be san sanda ya danna power button ya kashe wayar gaba daya ba. Sai kuma yayi murmushi tunanin abinda ya aikata na dawo masa, da kunya matuka amma ya zai yi? Hakan ya kamata dama tun farko, ya kuma tabbatar hakan ya farantawa Baban rai dan yadda yake masa magana zakaji muryar sa a sake take cike da annashuwa. ***Shiru shiru be fito ba, har ta gaji da tsaiwar ta zauna shiru, mikewa tayi tana kallon kofar da ita kadai ce a cikin falon, nan kuma taga ya shiga, yanke shawara shiga ciki tayi kawai dan ba zata yi ta zama ba. Kofar ta bud'e a hankali ga mamakin ta sai taga wani falon nan dan karami sai kofofin dake ciki, wadda take kallon ta, ta nufa ta murd'a a hankali ta tura kanta, sukayi ido biyu dashi idon sa akan kofar, saurin sakin handle din tayi zata koma muryar sa ta dakatar da ita "Zo nan." "Na'am?" "Kinji me nace ai." Shigowa tayi ta tsaya daga hanya, ya kalle ta ya kalli Hijab din jikin ta. "Ki cire Hijab din kizo nan ki zauna." "Ba tafiya zamuyi ba?" "Kinzo kenan." Yace yana d'age mata kafadar shi "Toh ai na zanje na kwanta? " "A kaina." Yace mata kai tsaye, saurin kallon sa tayi ya d'aga mata gira, sai ta kauda kanta daga kallon shi cike da mamakin amsar da ya bata "Oya zo nan kafin na taso, kina bata min lokaci." Matsowa tayi tana turo baki, ya girgiza kai yana sake kishingid'a sai da tazo daidai in da yake a kwance, sannan yace ta cire Hijab din, ta dade tana wasa da Hijab din ta kasa cirewa shi kuma yana kallon ta, da k'yar ta cire sai ta yafa shi a saman kafadarta zuwa chest din ta. "Zauna." Ya nuna mata saitin cikin sa tunda shi a kwance yake, dan dosanawa tayi ta zauna duk a darare take, tashi zaune yayi yasa ta a tsakiyar jikin shi, numfashi taja da sauri tana kokarin gyarawa ya sauke kafafunsa kasa ta zama dai tana gabansa a zaune kafafun sa sun sakata a tsakiya, kunya da wani irin yanayi me wahalar fassarawa ta shiga, yayi kamar be san me yake ba, ya kai hannu zuwa saman kanta ya hau shafa mata gashin kanta da ya dade yana burin tabawa. Duk ta rikice ta kasa zama sai motsi take ta cigaba da abinda yake yi. "Ina ribbon din?" Ya rad'a mata a kunnenta, tayi saurin bud'e jakar ta ciro ta mika masa, yayi murmushi ya kama gashin ya saka mata, be yi sosai ba tunda ba wai ya iya bane dama, tana jin shi yana cirewa yana sake maidawa a dole sai ya kama shi da kyau. "Gashin doki ne?" Yace bayan ya gama daidaitawar a ganin shi _"Na jaki ne."_ ta fada a ranta, amma a fili shiru tayi kawai dan ko yayi tayi motsi sai taji ta a jikin sa gaba daya. Maimakon da ya gama ya barta ta tashi sai yaki, suka cigaba da zama a haka. Ya kunna wayar sa dake gefen su, ya kira Ishaq dan dama dazu yaga missed calls dinsa yana tuki lokacin. A handsfree ya saka wayar bayan Ishaq din ya d'aga, suka gaisa sannan ya tambaye shi amarya dan Tariq din ya fada masa in brief, "Kana da matsala." Yace yana girgiza kansa "Matsalar me? Daga cewa ya amarya? Ai wallahi kai dan gata ne, ga gida ga mota ga mata wallahi ka godewa Allah." "Akace maka ban gode ba?" "A ah kawai dai tuna maka nake ne, yawwa dazu ma Yasmin ta kirani zata dawo cikin week d'in nan har tace na fada maka." Gaban Jidda ne ya fadi, jin an ambaci sunan Yasmin, ta yunkura zata tashi ya sake matsewa yana zagayo da hannun sa ta cikin ta. "Karka dameni da magaanar wata yarinya pls." "Ai dole na isar da sakon ta, ka sani ko da ita zakayi ta biyu? Yarinya me so da kaunar ka." "Ni bana son ta." "A ah fa, kar reshe ya juye da mujiya, ka sake tunani sosai." "Idan ka shirya waya dani ka kira." Ya katse kiran yana jan siririn tsaki, hannun sa dake cikin Jiddan yasa ya shafa cikin nata wanda yake flat kamar ba'a taba saka masa abinci ba. "Bakya cin abinci ne?" Banza tayi masa dan baki daya wayar da taji yanayi ta sakata a yanayi, gumi ne ma yake ta keto mata ta cikin jikin sa. "Dole ki dinga cin abinci sosai, naga alamar bakya son ci shiyasa, ji cikin ki, wannan ai sai na balla shi." "Zanje na kwanta." Tace a muryar haushi "Oya kwanta mana, waya hanaki?" "Dayan dakin zanje." Tace Sakin ta yayi yana ware hannun sa, ta tashi da sauri ta fice. Lumshe idon sa yayi ya bud'e, be san dalilin da yasa yake acting haka, ko dai magaanar Mama gaskiya ce son Jiddan yake? ***Dayan dakin ta shiga, ta jefar da Hijab din da jakar hannun ta, ta zauna tana kallon kofa, "yarinya me son ka da kaunar ka" ta tuno abinda na wayar yace, "ka sani ko da ita zakayi ta biyu?" Wani kululun abu ne yazo ya toshe mata a wuya, tana son ya Tariq sosai dan bata sake gane tana son sa ba sai da ta samu kusanci dashi sosai, ya iya duk abinda yasan zai tafi da hankalin mace, in a cool and matured way, ko kallon ta yayi sai taji wani iri bare yayi mata magana, closeness dinsu shi yafi komai taba ta. Duk da tasan baya son ta kamar yadda take son shi, amma zuciyar ta, taki barin ta, ta cire shi daga cikin ranta. Tsawon mintuna arba'in tana nan a zaune a wajen, dan bata da shirin tashi ma, ta saka wannan da kwance wanchan hankalin ta gaba daya yana wajen sa, ko ya cigaba da wayar sa ko ma ya kira wadda aka kira da sunan Yasmin din duk dama pretending yake da yace baya son maganar, tasan kadan daga aikin maza,toh amma ita a matsayinta na wa da har zai yi pretending a gaban ta? Ai bata jin tana da wannan matsayin ma baki daya. Kitchen ya nufa bayan ya fito daga dakin, yaje ya dauko yoghourt ya duba akwai ragowar cake din da yaci da safe, ya samu silver cup ya hado mata dashi ya nufi dakin nata, ya kwankwasa tayi saurin gyara zaman ta, ya turo ya shigo rike da plate din, kin kallon sa tayi ya ajiye ya kasan rug din gaban gadon ya zauna yana tankwashe kafarsa "Ga dinner, na duba bamu da komai a kitchen din." "Na koshi." "Wallahi karya kike, sai kinci kuma." "Ikon Allah." "Ikon gaske, sakko malama, bana son iyayi." Yace yana gimtse fuska, kaamar zatayi kuka ta sakko, ya matso daf da ita har kafarshi na gogar tata,daukar cake din tayi ta soma ci cikin k'asa kasa da murya yace "Ki cinye tatas so nake cikin nan ya dago ko kad'an ne kar kizo ki kasa daukata." Kwarewa tayi jin abinda yace, ya tashi da sauri ya kawo mata ruwa tasha, kanta a k'asa ta dauki yoghourt din tana sha tana kallon dayan side din, gaba daya ta gama gano ya Tariq bashi da ta ido ko kad'an, idan ya fadi wata maganar sai ka rantse bashi ne yafade ta ba, kuma ya fuske kamar be yi ba. A hankali ta shanye yoghurt din, ya dauke plate din ya fita ita kuma ta shiga toilet dan ta gyara bakin ta, ta dauka idan ya tafi ba zai dawo ba, tana fitowa ta sameshi a zaune ya kunna system dinsa ya dora ta akan kafarsa, gefen sa bakin shayi ne yana fitar da tururi. "Menene size din underwears dinki?" Ya tambaya idon sa na kan system din, jin tayi shiru ya sashi dagowa "Zan gane size din dayan da na gani dazu a wardrobe dinki." Yace yana mata shu'umin murmushi. *_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_* _(Where every flavour tells a story .....)_ *_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_ _08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_ _INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*? GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_ _MU NA YIN:_ *_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_* *_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_* *_LOCAL DRINKS:_* _HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_ _MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._ _KADA KU MANTA MUNA YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._ _FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_ _ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_ _PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_ [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (37) ***A hanya Baba ya sake kiran sa, yace masa gashi nan ya taho, ya katse kiran sai ya kira Fauwaz, yana tare da Maama lokacin tana masa magaanar daurin auren da kuma abinda take so yayi mata saboda bakin ta, manyan bakin da zasu zo gidan. Daga wayar Tariq din yayi dan dama yana so ya kirashi sai kuma wani abun ya dauke masa hankali, "Kana ina?" Yace yana dagawa "Wajen Mama, ka zo ne?" "No yanzu dai zan shigo gidan, bari na karaso." "Ok." Ya katse wayar "Tariq ne?" "Eh shine." "Daga ina zaizo? Dama ba a gidan ya kwana ba?" "Eh toh ban dai sani ba, amma inaga a gidan sa ya kwana." "Oh okh, kace ina jiran sa fa." "Ok ma, bari na je na karasa shiryawa dan Baba yace baya so bakwai tayi bamu tafi ba." "Ok, shikenan." Juyawa yayi ita kuma ta wuce kitchen taga abinda ake yi, duk da komai da za'a ci a bikin order akayi amma kuma akwai aikin da ake mata a kitchen shi zata je ta duba. Murmushi Fauwaz yayi bayan ya baro wajen Maman, dan yasan bata san Tariq ya aikata tsiyar ba, kuma yasan idan ta sani akwai matsala sosai, su dai yan kallo ne, gefe zasu koma suka yadda zata kaya. Kallon gate din da aka bude yayi, Tariq din ne, ya shigo ya samu gefe yayi parking Fauwaz din ya karasa wajen motar  ya bud'e masa kofar, ya zuro kafarsa bayan ya fito rike da kayan sa, ya mikawa Fauwaz din. "Ajiye min a ciki ina zuwa, zan ga Baba." "Ai tun asubah be shigo ba fa, sai dai Mama ita ce take neman ka dama." Hannu yasa ya karbi kayan yace "Bari na fara shiryawa toh, samo min plain tea nayi warming ciki na." "Ok." ***A gurguje ya shirya cikin shigar farar shadda wadda da akayi wa aiki da bakin zare, tea din ya dauka yana sha da hannu daya, dayan hannun kuma yana daidaita hular kansa, kiran sa akayi a waya ya daga da sauri dan yasan Baba ne, sukayi magana ya ajiye cup din ko rabi be sha ba, ya rige babbar rigar a hannun sa bayan ya saka bakin takalmin sau ciki, ya fito da sauri ya nufi bangaren Maman, part din nata a cike yake sai yaji duk ya takura, Amira da tazo zata fita yace tayi wa Maman magana. "Ta shiga wanka." Tace tana kallon yadda kayan jikin sa sukayi masa kyau "Ok, kice mata mun wuce." "Ok sai kun dawo." Har yayi gaba itama ta wuce sai ya tuna "Amira." "Na'am?" "Anjima driver ya kaiki wajen Jidda." "Tana ina?" "Ban sani ba." "Wallahi Ya bansan ina ba shiyasa na tambaya." "Gidana toh." Saurin toshe bakin ta, tayi alamun laaa, sai tayi dariya, hararar ta yayi yana kallon ta, tayi saurin daina dariyar yace "Saura kuma ki bud'e bakin nan naki ki fada wa mama, zan yi magana da ita idan na dawo." "Ba zan ma fada ba wallahi, ni yanzu ma zan tafi sai na dawo anjima kafin lokacin event din yayi." "Event din me za'a yi?" "Anan gidan ne zaa yi, itama Jiddan ta sani ai kayan da zata sa ma yana waje na." "Ba zata zo ba, kije dai ke sai ki dawo anjima din." "Toh shikenan bari na chanja kayana, zan ce ma Mama na je a sake gyara min gashi sai na tafi chan." "Gyaran gashi? Aina akayi?" "Glamorous Saloon ne, duk fa yau zamu je da Jiddan dama." "Ok kuje tare din, a gyara mata sai ku koma gida." "Ok tam." "Kice mata nace ta saka Hijab idan zaku fita." "Toh Yah." Tace tana gimtse dariyar da take neman taho mata, juyawa yayi da sauri ya bar wajen, ta kwashe da dariya ta buga tsalle. Kaamar yadda tace masa zata fadawa Maman haka tace mata, ta dauko ATM din ta, ta bata ta fito wajen takwas bayan su Ya Tariq din sun tafi, ta samu Sam tace ya kaita gidan  Tariq. Jidda na kwance a falon bayan ta gama kukan bakin ciki ta hakura gashi bata ga wayar ta ba, bare ta kira ko Aunty ce tasa ta roke shi taji ana knocking, tashi zaune tayi ta tabbatar da knocking din ake ko kunnenta ne sai taji an sake kwankwasawa, wajen kofar taje tace waye? Da sauri ta bud'e jin muryar wadda bata yi zato ba, suka rungume juna suna ihu kamar wadanda suka shekara basu ga juna ba. Zama sukayi a kujerar Amira ta kalli falon "Haduwa, ashe kina nan." "Dama zaki zo?" "Gashi kuwa, Ya Tariq ne yace nazo na kular masa da matar sa." "Ba wani nan, ni kyale ni kinsan ya ce wai bazan je gida ba, dan Allah haka ya dace?" "Kinsan fa shi daban yake, wallahi dan zaki sha fama." "Allah sarki ni." "Wai yaushe kika taho? Kuma kin taho gaba daya kenan?" "Oho nima ban sani ba, bansan me suka kulla shi da Aunty da Yaya ba, yazo ya tiso keyata a gaba har kuka sai da nayi wallahi." "Ai Ya Tariq, sai a barshi wallahi, haka ya hanaki dinner kina ji kina gani." "Ki daina tuna min dan Allah." "Toh sorry, tashi zakiyi ki mana wani abu mu dan ci ko breakfast ban yi ba, yace muje a gyara miki gashin kanki." "Gashi kuma? Ni ai bana retouching." "Eh ai ba retouching ba, sake dai gyara mishi kayanshi zaa yi." "Kayan shi?" "Eh mana, baki sani ba?" "Ke kika sani, ta yaya gashi na zai zama kayan shi tsakani da Allah kema dai banda neman magana." "Ah toh na waye dah? Lallai ma ke din nan wallahi." "Oho ke kika sani, babu komai a gidan nan sai dai kisha tea da cake." "Anjima ai za'a kawo garar, wai hadda Ya Tariq a garar da Baba yayi." Ta kwashe da dariya, "Ko da yake yace shi yarsa yayi wa ba Ya Tariq ba." "Allah sarki babanmu, Allah dai ya saka masa da gidan aljanna." "Amin Amin. Muje ki shirya dan da wuri zan koma kar abubuwan su hade min, amma zan dawo da daddare idan kina so." "Eh dan Allah ki dawo, wallahi inaso ko kwana ne ma kiyi." "Wa? Ni? Tabdijam, Ya Tariq din ne zai barni na kwana?" "Me zai hana?" "Ba za'a ji mutuwar sarki a baki na ba, jeki shirya dai bari na sha tea din." "Kyaji da gulmar ki." Tace tana yin gaba ta shiga kofar da zata kaita dayan falon kafin dakunan nasu. Wanka tayi a gurguje ta ciro riga da skirt ta saka ta dauko veil dinta da handbag ta fito ta samu Amiran ta kunna TV tana kallo tana shan tea din "Kira min wayata inaga a gida na barta." "Ok." Kitchen ta wuce ta hado tea din tazo ta zauna lokacin da amira ta kira wayar tata, "An d'aga gashi ." Ta mika mata, karba tayi ta kara wayar a kunne "Hello aunty?" "Uncle ne ba Aunty ba." Da sauri ta ciro wayar daga kunnen ta, ta kalli number din, taga dai number ta ce, "Waye?" Amira tayi mata alama da hannu "Dama wayata nake nema shine nace Amira ta kira min ita." "Oh okh, tazo kenan, kin daina kukan?" "Umm.." "Good, akwai wani abu ne?" "Um um." "Okh sai mun dawo." A ciki ta amsa ya kashe "Wai wa ya daga?" "Ya T..." Tace tana mika mata wayar ta "Wai kina nufin da wayar taki ya tafi." "Gashi nan, ni ban masan yaushe ya dauka ba." "Lallai Ya Tariq, ai kamar akwai landline a hanyar kitchen din chan, na ganta a saman wani table." "Ni wayata nake so,." "Kika sani ko new one za'a kawo miki." "Ai bance inaso ba." "Malama ki daina pretending dan Allah, Amira ce fa, your best friend mene wai ban sani ba,ko yanzu kin daina son Ya Tariq din ne ake bashi I don't care attitude." "Ni da nace miki ina son sa ne?" "Fadawa wanda be sani ba." "Tashi mu tafi, kar ya dawo yace ya fasa." "Kad'an daga aikin babban Yaya." Ta mike zata yafa mayafi Amira ta tuno da abinda yace mata "Wallahi na tuna,yace karki yafa mayafi wallahi" "Na shiga uku, mayafin ma?" "Wallahi haka yace mun, kuma yana sane sai ya tambaya." "Gaskiya ni wallahi." "Haka zaki hakura, dole abi miji dan a zauna lafiya." "Ke kika sani." Ta suka fito, Sam yana zaune tare da gate man yana jiran su, suka shiga motar yaja suka bar gidan. Ita aka fara yiwa sannan akayi Amiran, sai sheki gashin yake da kyalli musamman ita da take da gashi sosai, ita kanta me salon din sai da ta yaba da tsantsi da yalwar gashin ta, duk da bashi da cika sosai tsayin da tsantsin ne gashi baki sosai. A gate aka ajiyeta Amira tace ba zata shigo ba su Salma suna ta kiran ta, kamar zatayi kuka haka ta shiga gidan tana cike da jin haushin Tariq din. *_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_* _(Where every flavour tells a story .....)_ *_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_ _08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_ _INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*? GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_ _MU NA YIN:_ *_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_* *_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_* *_LOCAL DRINKS:_* _HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_ _MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._ _KADA KU MANTA MUNA YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._ _FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_ _ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_ _PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_ [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (38) ***Bayan la'asar suka dawo, yana shiga gida ya dauki motar sa ko ciki be shiga ba dan yasan Maman ma tana cikin mutane ya wuce nasa gidan, baki daya wunin ranar tunanin ta yayi tayi, shiyasa suna sauka yayi gidan ya huta gaba daya a chan duk da anjima dole ya dawo gidan nasu kafin a tafi kai yaran. Horn yayi aka bud'e masa ya shiga da motar ya samu gefe yayi parking sannan ya fito, hannun sa rataye da babbar rigar da bata fi awa daya a jikin sa ba ya cire ta dan duk a takure yake. Key din ya mikawa faisal ya haura, ya murd'a kofar yaji ta a rufe sai yayi knocking. Idar da sallar ta kenan dan bacci tayi tun da tayi azahar ta kwanta sai lokacin ta tashi, tayi sallar tana zaune jigum tana tunanin yanzu su Amira suna chan ana shan shagali ban da ita, da tuni tana part din Yaya ana ta harka. Knocking din ya sake yi ta tashi daga wajen da take ta nufi kofar ta bud'e ta, yana tsaye hannun sa rike da wayar ta da tashi sai babbar rigar dake sakale da dayan hannun, matsawa tayi ta bashi hanyar ya shiga ciki ta rufe kofar ta juyo ciki. Har ya zauna a kujera ya ajiye wayoyin a gefen sa, ya cire hular kansa yana dan kishingid'a saboda yadda yake jin gajiya. Bata ce masa komai ba, ta wuce kitchen ta dauko ruwa da cup ta kawo masa sannan ta mike ta shige ciki, ruwan ya dauka yasha ya dauki remote ya kunne TV ya mike kafarsa sosai sannan ya karo AC falon. Dakin taje ta zauna kurum tayi shiru tana tunanin me ya kamata tayi,shima kuma kamar wanda aka kullewa baki be ce mata komai ba, sai duk taji babu dadi dan ta dauka zai yi mata magana tunda dai shi ya ajiye ta. Ta dan dade a zaune sai kawai ta tashi tace bari ta watsa ruwa duk da tayi da suka fita da Amira, amma kuma baccin da tayi taji tana bukatar ta watsa ruwan dan duk zuciyar ta a jagule haka ta tashi. Tana shiga wankan ya shigo dakin, ya zauna a gefen gadon rike da wayar ta da ya kawo mata, motsin ruwa yaji a toilet ya gane tana ciki, maimakon ya fita sai yayi zaman sa idanun sa na kan kofar toilet din yana danna wayar sa. Sam bata ji shigowar sa ba, shiyasa ta fito kai tsaye daga toilet din daure da towel din da yayi amfani dashi dazu, kanta a rufe da karamin towel saboda kar ruwa ya taba. Sai da tazo kusan rabin dakin sannan ta ankare dashi, tayi diri-diri duk ta diririce kamar zata koma sai kuma taga shima komawar da kunya, tsayawa tayi chak kawai a wajen da take ta sunkuyar da kanta k'asa "Ga wayarki." Yace yana daga mata ita sama idon shi na kan ta "Zan dauka." Tace tana jan towel din a kokarin ganin ta sake rufe jikin ta sosai "Zo ki karba, ko na koma da ita." "Ni ba amfani zan da ita ba." "Ba wani, Aunty ta kira ki, sannan Amira tayi miki text wai zasu zo, na kirata nace bana neman su." "Toh ka fita idan na saka kayan zan fito sai na karba." "Ba in da zani." Yace yana gyara zaman sa, motsawa tayi daga in da take tsaye a hankali har ta isa wajen wardrobe dinta, ta zaro Hijab zata saka ya mike ya iso ya rike Hijab din yana mata kallon cikin ido "What are you try to hide?" Shiru tayi dan yadda ya matso so close da ita, ya hana ta motsawa yana kuma yi mata kallon k'asa-k'asa. "I'm asking you, me kike boye wa, show me." "Dan... Allah... Kayi hakuri.". Ta fada a rarrabe ganin ya rike jikin towel din, murmushi yayi yana cije saman lips dinsa, ganin yadda duk ta firgice ta shiga tashin hankali. "Kema wai kin girma ko?" "Dan Allah ni dai kayi hakuri." "I can't, haram ne?" "Eh." Tace da sauri ba tare da tasan ma ta fada ba. Kallon ta yayi da sauri still yana rike da gefen towel.din itama ta rike kakam "Ta ya akayi ya zama haram?" Ya kai hannun sa saman kanta ya cire towel din da ta daura ta rufe gashin "Wow." Yace yana ya saka hannu ya shafa gashin "Ta ya akayi ya zama haram? Fada min." "Sanyi nake ji, ka tsaya nasa kaya na, dan Allah." "Ok, ok.. Saka toh." Ya cika towel din ya jingina da jikin mirror yana folding hannayen sa "Kaje waje." "Ba in da zani, idan zaki sa kisa idan kuma sai na taimaka miki fine, I will be glad to help." "Na shiga uku." "Da saura ma yarinya." Ya kad'a kai yana murmushi. Doguwar riga ta dauko ta dora ta akan towel din sannan ta zare towel din ta kasa, ta saka Hijab din akai. Dariya ta bashi yadda take ta sauri ta gama ta kai towel din ciki ta sakashi a washing machine, sannan ta fito "Kin manta baki saka abinda na gani a cikin wardrobe dinki ba, da twin dinsa." "Bra and pant." Ta fada a zuciyar ta, Da sauri ta fice daga dakin dan ta gano Ya Tariq so yake sai ya hanata sakat a gidan. Dariya ya saka, ya mike daga jinginar da yayi yabi bayan ta, ya sameta a kitchen kamar be neman abu. Hannun sa zube a cikin aljihun sa ya tsaya a kofar kitchen din yace "Kije ki shirya sosai, ki sameni a mota." "Gida zamu?" "Oho, don't waste my time." Da sauri ta koma dakin, ta dauki underwears din ta koma toilet ta saka sannan ta saka riga da skirt sakakku ta dora veil akanta me dan kauri dan bata so yace mata lallai sai ta saka Hijab. Flat shoe ne a kafarta duk da bata da tsawo chan amma shine raayinta, shi ta saka ma yanzu ta fito ta same shi a zaune a mota yana amsa waya ta cikin kunnen sa dake sakale da Bluetooth. Tana zama ya dora mata wayarta akan cinyar ta, ta dauka ta jujjuya ta, sannan ta kunna ta hau whatspp dan ganin me yake faruwa. Wayar yake tayi idanun sa na kan titin ko sau daya be juyo ya kalle ta ba, har suka karasa gida, da murnar ta,ta kalle shi shima a daidai lokacin ya juyo bayan ya gama wayar wadda da dukka alamu akan aikin sa ne. "Ki ajiye wayarki kusa dake, zan kiraki." Yace bayan ya samu waje yayi parking zata fita, gid'a masa kai tayi ta fita daga motar yana kallon ta, sai da taga ta fita sannan ta kalle shi "Ba zan koma ba." Sai tayi gaba da sauri ta shige part dinsu, dariya ta bashi ma, ya kada kansa yana hasaso yadda zai ciccibeta idan har tace zata masa gardama. Fita ya sake yi daga gidan dan zuwa ya samu Baba a chan guess house dinsa. Babu kowa a part din nasu sai masu aiki duk suna chan bayan gidan in da ake taron bikin kafin azo kai amaren gidajen su, Amira ta kira a waya tace ta kawo mata kayanta, sai gata ita da Nu'ayma, ta saka suka fita Amira na tsokanar ta. Aunty ce ta hango su da suka taho wajen, ta kalli chan in da Maman take taga tana wani abun bata lura da Jiddan ba, tashi tayi ta riga su isa ta kama hannun Jiddan tace musu tana zuwa. Chan wajen da ba mutane suka je Jiddan ta gaishe ta, ta amsa cike da murnar ganin ta "Ashe da gaske yake da yace zai kawo ki." "Kece kika ce ya kawo ni?" "Eh nice, sannan Baban ku ma yana son hadaku gaba daya yayi muku magana har Maman Fauwaz, ki nutsu ki kwantar da hankalin ki, duk abinda zai je ya dawo ki rike mijinki kinji? Karki ji tsoron kowa." "Aunty menene? Akwai matsala ne?" "Babu ko daya, nasan ba lallai ta amince da tarayyarku ba, musamman yanzu da duk muka gane Tariq yana son ki, zatayi kokarin baki matsala dole sai kin jajirce sannan ki hada da addu'a,." "Wallahi ni Aunty tsoro nake ji." "Babu abinda zai faru kinji? Ki kwantar da hankalin ki." "In sha Allah, nagode." "Muje ciki, kije ki gaishe su ki dake kuma, mahaifiyar mijinki ce ta zama dolen ki." "Toh." Tace a sanyaye, suka koma ciki Mama ta hango su, ta gimtse fuska sai taga Jiddan na tahowa in da suke a zaune da manyan kawayen ta harda matar gwamnan adamawa da matan manyan koshoshin kasar "Jidda." Aunty Mimi ta tare ta tana kusa da in su Maman suke dan suna jin su ma "Laaa, ina wuni?" "Lafiya Lou, ban ganki ba gaba daya a kwana biyun nan, har Amira na tambaya tace kina nan." Murmushi tayi bata ce komai ba, "Karasa wajen su Maman ki gaishe su." "Toh." Tace tana matsawa wajen su, ta russuna har k'asa ta gaida su, suka amsa a sake banda Mama da ta juyar da kanta gefe tana magana. "Matar Tariq ce, shine babba a yaran Mama." Aunty Mimi tace musu tana murmushi "Ah Hajiya Aisha har suruka ce dake amma bamu sani ba? Gata nan Masha Allah wallahi." "Kun sani yanzu ai." Tace tana dariyar yak'e, gefe kuma kamar ta jawo Aunty Mimi da Jiddan ta hada tayi musu shegen duka haka taji, tashi Jiddan tayi ta koma chan wajen su Amira, kafin daga bisani ta fice daga wajen ta tafi dubo Hajiya Yaya. Da murnar ta,ta shiga kamar wadda ta dade bata ga Yayan ba haka taji, itama Yaya na ganin ta, ta dire abinda yake hannun ta "Wa nake gani kamar matar malam nabahani." "Kai Yaya?" Ta kwashe da dariya "Toh Badamasi." "A ah Yaya, ba ruwana wallahi." "Ah gaskiya, kya tarewa miji wai ke dadi miji daga kwana daya har ya hure miki kunne ko?" "Kai Yaya!" "Allah kuwa, kin yi luf dake a dakin miji, yar kumama an san dadin aure." "Na shiga uku, Yaya daga zuwa na?" "Zuwan kenan?" Tace tana dariya "Eh Yaya." "Ai da naji shiru nace munafukan yara kaji su luf kamar basa duniyar nan.". "Tsokanar mu dai kawai kike Yaya." "Yo Allah ,shima munafukin yana fuffukar baya so baya so ashe duk munafurci ne." "Me zan samu ne Yaya? Yunwa nake ji." "Na shiga uku ni Hajara, ba dai horon yunwa yaron nan yayi miki ba, kai ni sai naga ma daga jiya zuwa yau kin fada sai uban fari da kika kara, gaya min gaskiya me yayi miki?" "Innalillahi, Yaya ba komai fa, kawai dai abincin gida nake son ci, shiyasa, amma a kwana daya Yaya sai mutum ya chanja? Jiya ma fa muna tare." "Toh ai abun nasa ne, kinsan kan sa da motsi har yanzu, sai kin yi hakuri dai." "Hajiya Yaya kenan." "Iya gaskiya ta na fada miki, tashi ki duba kitchen akwai flasks din abincin da Babar taku ta aiko, sai ki zuba ki cika cikin ki." "Yawwa yanzu naji batu." Ta mike ta shiga kitchen din ta zubo fried rice da chicken tazo ta zauna tana ci a hankali suna hira da Yaya. Har magriba tana wajen Yayan sannan su Amira suka shigo suke cewa Baba ya dawo ya saka a kira masa Ya Safiyya da Umaima part din sa, dan yi musu final nasiha tunda har masu zuwa daukar amaren sun fara zuwa. Kira ne ya shigo wayarta, ta kalli screen din taga an rubuta Capt.T, kai tsaye ta gane shine, ta daga a kasalance ta saka a kunnenta "Ina kofar part din Baba." "Na'am?" "Kizo." "Ok." "Ba zai shigo nan din ba? Ko da yake ina yaga idon da zai hada dani? Ai be isa ba." "Hajiya Yaya ta Ya Tariq." Amira tace tana dariya "Na Jidda dai, wace ni?" "Ai kece ta karfen." "Jeki dai dadi miji, daga kira har kin mike jiki na rawa, ba dan jan ajin nan, ko ni da nake ba yar zamani ba na iya jan ajin nan tun zamanin kakanku, shima yasan Dije ba ta wasa bace, shiyasa ya kasa yi min kishiya." "Yo ai ke Yaya surutun ki kadai sai ya kori kishiya." Amira tace tana dariya, ita dai jidda fita tayi ta bar su suna gamzawa, ta hange shi tsaye a kofar part din Baban tsaye shi da kaamar Mama, suna magana amma idonsa na kan ta tunda ta nufo su, a tsorace take dan bata yi zaton zai kirata Mama na wajen ba, bata san me zata tarar ba, shiyasa ta dinga jan kafar ta, har ta isa wajen kanta a k'asa tayi sallama, shi kadai ya amsa ta kalli Maman wadda fuskar ta, take a matukar hade kana gani kasan ranta ya kai kololuwa a baci, bud'e kofar tayi ta shige, ya girgiza kai kawai yana kallo na, fuskar sa babu yabo babu fallasa amma ya nuna kamar ransa babu dadi. "Muje." Yace yana nuna mata hanya, a tunanin ta part din Baban zasu shiga, amma sai taga ya nuna mata hanyar wajen da akayi parking motar, jiki a sanyaye tabi bayan sa, ya bud'e mata bayan motar ta shiga sannan shima ya shiga, sam yazo ya shiga wajen driver ya tada motar suka bar gidan. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (39) ***Cikin yanayin bacin rai Baba ya rufe ta da fada, ta in da yake shiga ba tanan yake fita ba, sosai ran sa ya baci akan abinda Maman tayi, shiyasa ya ki bari a kira Jiddan yace kuma Tariq ya dauki matar sa su wuce gida, ya kuma kafa masa sharadin duk abinda ya faru da ita sai ya basu mamaki shida mahaifiyar sa. Ranta a bace yake matuka bayan ta dawo ciki dan da Tariq din ya fita bin bayan sa tayi, ta tambaye shi dalilin da zai wulakanta ta haka har ya dauki Jiddan ba tare da sanin ta ba, hakuri kawai ya bata dan be san me zai ce ba, bata sake magana ba ganin Jiddan ta nufo su, sai kawai ta koma ciki in da ta tarar da Baban na yiwa Safiyya da Umaima nasiha. Tana shiga yace su tashi su tafi Allah yayi musu albarka, sai kawai tabi bayan su, suka fito yayi kwafa yana cike da haushin Maman, dan ta kaishi makura a yau zai kuma nuna mata shi yake da iko da ita da Tariq din, ba zai tsaya ta zubar masa da girma akan son zuciyar ta ba. Tafiya akayi dasu kowacce a nan Abujan zata zauna, duk da bacin ran da Maman ke ciki haka ta daure har aka tafi dasu, sannan tunanin ta ya dawo kan abinda ya faru, da irin maganganun da Baban ya gaggasa mata a gaban yaran. A daki suka sameta bayan sun dawo daga kai amaren, Aunty Nafi ta zauna a kubin ta, tana kallon yanayin ta "Wai Yaya me ya faru ne? Ko duk tafiyar yaran ce?" "Rai na ne a bace Nafi, wallahi." "Me ya faru?" "Kinsan wai ashe Tariq tun jiya ya dauki yarinyar nan suka wuce gidan sa?" Zaro ido tayi "Ba dai Jidda ba?" "Ita, ace ya kasa fada min sai yau zanji a wajen ubansu, tsakani da Allah me Tariq yake so ya zama ne?" "Gaskiya ba haka aka bar shi ba, Tariq din da muka sani daban wannan Tariq din daban, gaskiya an samu matsala, kema Yaya kin yi sanyi da yawa har kika bari haka ta faru, yanzu suna ina?" "Sun tafi." "Kika bar su kuma?" "Ya zan? Baban su yace wallahi komai zai iya faruwa idan nace zan wani abu." "Tab! Amma gaskiya da matsala, shikenan haka zamu zuba ido kishiya ta mallake miki babban d'a?" "Ba zai yiwu ba ai, wallahi ba zan amince ba, duk tsoratarwa kawai yake shima, dole na tashi a tsaye." "Gaskiya dai, ai ba zai yiwu ba." "Menene shawararki?" "Eh toh, tunda dai a yanzu ran Honourable ya baci sosai, zai iya aikata komai, ta karkashin kasa zamu biyo musu, tunda dai ke bakya son dan tainakon nan na wajen malamai." "A ah bana so, wani abun dai daban." "Yaushe Baban zai yi tafiya?" "Jibin nan zasu tafi tare da Halima." "Wannan karon kuma? Ah lallai kinyi sake wallahi." "Ni duk wannan baya gaba na, ta d'ana nake." "Toh kawai mu tura musu Salma da Amira gidan, tunda dama hutu suke dukkansu, sauran aikin sai mu barwa Salma tasan me zatayi duk zan dora ta akan komai." "Kina ganin hakan zai yi? Amira fa bata da aminiya irin ta." "Duk wannan ba matsala bace ai, ke dai ki bar komai a hannu na." "Shikenan, dan Allah ayi duk yadda za'a yi, kafin ma a samu matsala wani abu ya shiga tsakanin su, yazo shima ya tattara ya tafi dan inaga a karshen satin nan zai koma Canada, dan naji Baban yana maganar suna ta masa mail ya ma kara sati,." "Toh kinga in da aikin ki zai shigo, ki masa lamfo-lamfo ki nuna masa komai ya wuce zaki kula da ita ko baya nan, daga nan ita kuma sai mu nuna mata shege." "Shikenan zan daure, yanzu ke yaushe zaki koma?" "Ai ban ga ta tafiya ba, sai naga yadda aka yi, ba a barki ke kadai ba, amfanin dan uwan kenan." "Toh kar mu bar Mimi taji maganar nan, zata bata komai." "Wa?* Ta kama bakinta "Ba zata ji komai ba, uwar iyayi sai ta hau fada mana magaana, kyaleta kice wani taro zan rakaki." "Shikenan, Nagode sosai, sai kuyi magana da Salman, shi kuma Tariq din nasan yadda zan masa, Dan ba karamin aikin sa bane suna zuwa ya koro su wallahi." "Zai aikata, musamman yanzu da baya ganin kowa sai figaggiiyar yarinyar nan, me zubin yunwa." "Wallahi ko ganin ta kusa dashi bana son yi, dan dai yaran yanzu ne, baka isa dasu ba." "Ba a hayyacin sa yake bane aj." "Toh Allah yasa ya dawo hayyacin nasa, kar a samu matsala kiji ana amai an samu juna biyu." "In sha Allah hakan ba zata faru ba, ina Allah ma ya kiyaye." "Toh Amin." Tace a sanyaye ***Tunda suka dauki hanyar babu wanda yace uffan, shi gaba daya hankalin sa na kan abinda ya faru da yake ta gudu tsakanin iyayen sa, gashi be san yadda Mama zata dauki abinda ya farun ba, gashi shi kansa be san dalilin da yasa ya kafe ba har yake ganin Baban yafi ta gaskiya. Be so hakan ta faru ba, yafi so duk su fahimci juna tunda an riga an daura auren. Yana parking ya fice daga motar be ko kalli in da take ba, a hankalin ta bud'e kofar ta fito, jikin ta da yayi matukar yin sanyi taja zuwa cikin gidan tana ayyana abinda ya sashi a cikin yanayin da yake ciki. A tunanin ta zata ganshi a falo, sai taga wayam alamun ya shige ciki, mayafin jikinta, ta ajiye a saman kujerar ta nufi kitchen tana kallon hanyar dakin nasa, ta leka store taga an kawo musu kusan komai an lode, kayan abinci na ban mamaki dan kar tayi karya da sai tace babu ce kawai babu a ciki. Wucewa still idon ta na kan bedroom din nasa, ta bud'e nata ta shiga, ta ajiye komai a mazaunin sa sannan ta sauya kayan jikin ta zuwa riga 3 quarter da dogon wando wanda ya dan tsuke daga sama ya bud'e daga kasa, headband ta dora akan ta fito zuwa kitchen dan sama musu abinda zasu ci, tayi kuma amfani da damar wajen zuwa ta gano halin da yake ciki dan ko motsin sa babu. Dankali ta dauko ta feraye ta soya ta hada da fresh chopped tomatoes, peppers, carrot da onions, tayi mixing tayi seasoning nasa sannan ta dama masa oat dan taga alamun yana so sosai. A tray ta dora komai ta nufi dakin nasa, har taje kofar zata yi knocking sai tayi wani tunani, fasawa tayi ta wuce nata dakin ta ajiye tray din a gefe ta dauki turare ta feshe jikin ta dashi sannan ta yafa matsakaicin mayafi a kan kayan jikin ta, sannan ta dauki tray din ta nufi dakin nasa. Yana zaune akan sofa be cire ko takalmin dake kafarsa ba, gaba daya tunanin sa ya kare ya rasa me yakamata yayi, wa kuma ya kamata dole yayi wa biyayya ya farantawa a cikin su, kowanne a cikin su idan yayi masa ya bar daya be kyauta ba, zai kuma saka kansa a matsala ne, gefe daya kuma baya jin zai iya rabuwa da ita kamar yadda Maman take da bukata ba, sosai yake jin ta a ilahirin gaba daya zuciyar da ruhin sa, kamar idan ya rasa ta yayi wani babban rashi me girma a cikin rayuwar sa, sai yake jin kamar ta dade da shiga rayuwar tasa sani ne be yi ba sai yanzu. Idanun sa akan kofar sanda ta kwankwasa, ya kasa motsawa ballantana ya bud'e baki yace a shigo, sake knocking din tayi a hankali kaamar me tsoron taba kofar, cikin muryar sa da ta shige chan ciki yace "Shigo." A hankali ta murda handle din sannan ta turo kofar ta shigo rike da tray din, idanun su suka sarke waje daya, ita tayi saurin janye nata dan hango wani irin abu kwance a cikin kwayar idon nasa, wadda ta kasa fassara yaren da yake kwance a cikin ta. A gabansa ta durkusa ta ajiye abun hannun ta, sannan ta mike zata juya yayi saurin riko hannun ta. "Ina zaki?" Yace yana mata kallon k'asa-k'asa "Kitchen, na manta ruwa da lemo." "Akwai ruwa a wannan fridge din." "Toh juice din fa?" "Bana bukata, sai dai idan zakiyi wani abun." "Eh zanyi." Tace da sauri, cikata yayi ya zamo kasa gaban tray din, ya bud'e plate din ita kuma ta juya ta bar dakin da tunanin ko zai dakatar da ita, amma sai taji be ce mata komai ba. Falon ta koma ta dinga zagaye haka kawai ta rasa me zatayi, daga karshe ta hakura ta wuce dakin ta, idon ta akan nasa dakin. Sai da ya gama cin dankalin da yayi masa dadi sosai, yasha oat dinsa ya wanke bakin sa da mouth freshner me dadin kamshi kamar mint, sannan ya jawo cable din system dinsa ya jona a chargy ya shiga kan mails din da akayi masa yayi replying wanda zai iya sannan ya duba available flight na karshen satin wanda zai bi, ya dade yana dudduba abubuwan da tsare-tsaren abinda ya kamata yayi kafin ya ajiye komai yaje yayi alwala yayi shafa'i da wutri, sannan ya cire kayan jikin sa ya rage dashi shi sai boxer da farar singlet ya nufi dakin nata. Rashin ganin haske a dakin ya sa ya gane tayi bacci kenan. Time ya kalla a wayar sa yaga sha daya har da mintuna, be san ya dau lokaci haka ba. A kanta ya tsaya ya dan haska fuskar ta da hasken wayar sa, bacci take tsakanin ta da Allah, gashin kanta da yazo har kusan rabin fuskar ta, yasa hannu ya gyara mata, ya durkusa a gaban ta yana kallon yar karamar fuskar ta gaba daya, so yake ya dan ja baya kad'an har ya samu amsar abinda yake so ya samu, ya kuma samu hanyar da Mama zata yarda ta amince da bukatar sa, baya so ya sabar mata da kanshi azo a samu matsala shiyasa yake son ya bi abun daki-daki. Saman kanta yayi kissing sannan ya gyara mata pillow da ke kanta a hankali yadda ba zai tashi ta ba, sannan ya mike ya fita daga dakin ya ja mata kofar. Da safe ta farka a tunanin ta zata ganshi a dakin, sai taga babu alamun ya shigo dakin ma kwata-kwata, tashi tayi jiki a sanyaye tayi abinda zatayi ta fito falon, tana fitowa yana shigowa sanye da kayan motsa jiki ya hada zufa sosai, damtsen hannun sa ta kalla tayi saurin dauke idonta, murmushi yayi k'adan ya zo saitin ta ya wuce ta gefen ta, ya shige ciki. Ajiyar zuciya ta sauke ta matsa tsakiyar falon tana duba abinda ya kamata ta sauya masa wajen zama, duk da babu datti ko kad'an amma sai da ta kara gyaran falon sannan ta shiga kitchen din. Toilet ya wuce kai tsaye yayi wanka ya fito yana goge jikin sa wayarsa tayi kara,ya sa hannu ya dauka ganin sunan Mama ya saka gaban sa faduwa, tattaro jarumtar sa yayi sannan ya daga. "Ina kwana Mama?" Yace bayan ya amsa sallamar ta "Lafiya lou, kun tashi lafiya?" "Alhamdulillah." Yace mamakin tambayar na kama shi "Toh Yayi, yaushe zaka fito?" "Anjima k'adan da nayi breakfast Mama." "Toh ka zo inason ganin ka." "Toh in sha Allah..." "Madallah..." "Mamma abinda ya faru jiya...? "A bar wannan magaanar, ya wuce kawai, ka cigaba da shirye-shiryen tafiyar taka, Allah ya taimaka ya bada sa'a " "Amin Mama." Yace muryar sa na bayyanar da tsantsar farin cikin da ya shiga. A gaggauce ya karasa shiryawa, be tsaya ko abinci yaci ba ya tafi. Tana kitchen taji fitar mota daga gidan, ta fito da sauri amma tuni ya bar gidan shi da Faisal. Wani iri taji ta tsaya rike da spatula tana jujjuya abinda yake faruwa a kanta. "Ko dai ya gama deciding rabuwa da itan ne?" Ta tambayi kanta, tunda dama ya fada ba sau daya ba sau biyu ba, ita ba spec dinshi bace ba, yanayin yadda ya d'an sakar mata shiyasa har ta fara samun hope, amma kuma idan ta tuna wasu mazan players ne na karshe, kuma zasu iya komai sai taji duk an dauke mata karsashin ta. A kasalance ta gama abinda take a kitchen din wanda take yi don shi yayi tafiyar sa ba ko sallama, juye komai tayi akan dinning ta wuce daki bayan tasha ruwan tea kad'an. Missed calls din aunty ta gani da ta koma dakin, ta kira ta bayan sun gaisa tace ta aiko Sam ya kawo musu abinci, tayi godiya suka ajiye wayar ta kwanta tana sake-sake a ranta har dai lokaci ya dan ja, sannan ta tashi tayi wanka ta saka wani silky material ta dan gyara fuskar ta da powder da eye liner sai lipstick ta dawo falon ta zauna tana kunna TV. Knocking akayi ta mike ta bud'e, yarinya ce ba zata wuce shekara goma ba, rike da flask sai wani babban basket a ajiye a gefenta,basket din Jidda ta dauka suka shiga ciki tana mata kallon rashin sani "Ya sunan ki?" Tace bayan ta karbi kayan hannun ta, ta ajiye a saman dinning "Godiya." "Sunanki kenan Godiya?" "Eh." "Ok..." Tace tana gid'a kanta, "Tace ki kirata wai." "Aunty?" "Eh." "Ok." Ta dau wayar ta kira Aunty, wai ashe sabuwar me aiki aka kawo mata, tunda Aunty taji Tariq din ma tafiya zai a karshn satin shine ta samo mata me aiki daga kauyen Abujan, ita Jiddan ma bata san tafiya zai ba, godiya tayi wa Auntyn tace yarinyar ta taso, ta zagaya da ita ta kitchen daga gefe kafin bq akwai daki da toilet a ciki, dakin yana da kofa ta cikin falon farko amma ginin kitchen ya dan boye ta,ta nuna mata a matsayin dakin ta. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (40) ***Kunsan sha biyu na rana tana zaune jigum har lokacin be dawo ba, abincin da tayi masa da safe ma sai Godiya ta bawa ta kai gate wajn masu gadi, sannan ta kara musu da wanda aunty ta kawo, taci ta zubawa Godiyan ta zauna tana kallon wani American movie har dai aka gama. Mikewa tayi a saman kujerar da nufin yin bacci taji an shigo gidan, da sauri ta tashi ta leka sai taga motar shi ce, tana tsaye jikin curtains din tana jiran fitowar sa sai taga Yaya ta fito tana magana tana kallon gidan, da sauri ta bud'e kofar ta fita, tayi tsalle ta rungume Yayan tana dariya "Yaya sannu da zuwa." Ta sake ta bayan ta tureta tana dariya "Bansan yaushe zaki hankali ba Jidda, karki zama kamar sauran shashasun chan mana." Tace "Murnar ganin ki ce fa Yaya, wallahi duk na gaji ni kadai kamar mayya a zaune." "Aure kenan yarinya, tukunna ma, akwai ciki da goyo." "Innalillahi Yaya." "Toh ai gwara ki sani, wuce ki kaini ciki kin barni a tsaye haka." "Laa na manta wallahi." Tace tana kama hannun ta "Dole ki manta, kai kuma idan ka gama zaman motar sai ka shigo ko?" Waigawa Jiddah tayi da sauri, yana zaune a motar ya zuro kafafun sa waje yana kallon su, kallon ta yayi daga kasa har sama haushin a yadda ta fito na tirnike shi, shiyasa yaki cewa komai dan kamar ma tunda ta fito bata ma lura dashi ba. Da sauri taja hannun Yayan suka shige ciki, gajeren tsaki yaja ya fito daga motar ya rufe yabi bayan su. Be shiryawa surutun Yaya ba, gashi ba zai iya hanata biyo shi ba da tace zata zo, so yayi ma ya kwanta ya danyi bacci kafin la'asar amma yasan honourable Yaya ba zata taba barin sa ba.    A tsakiyar falon ya tarar dasu Yayan ta zauna tana bayanin gidan da abinda be mata ba, ita dai jidda dariya kawai take taje ta kawo mata juice da ruwa ta zuba mata dan tasan minti kad'an aka kara Yayan zatayi complain. Zama yayi a daya daga cikin kujerun falon, ya bude hannunsa sosai yayi relaxing yana kallon TV "Muje ciki Yaya, sai kin fi sakewa." "Wa? Ni Allah ya raba ni da shiga dakin mijinki, naje nayi ubanme toh? Haram ba dani ba." "Kai Yaya, bafa nan ba." "Ko Ina ne ba zani ba wallahi, dakin ku zanje nayo me toh? A wanne dalilin ma? Kul naga kina kwasar mutane kina kaisu, baki ga yadda baban ku yake ba shi da yake da girma aka ma." Turo baki tayi duk kunya ta rufe ta, ita matsalar Yaya bata shiru sai kayi niyyar mata gwanin ta sai ta gwasale ka, yana jin su be tanka ba, yayi biris kamar baya wajen sai da Yaya ta gama sababin ta sannan ya dago ya zauna sosai yana kallon Jiddan, kallon kinyi min laifi, sauke kanta k'asa tayi yace "Yaya? Menene hukuncin mace ta dinga fita ba hijabi wajen wadanda ma Muharraman ta ba?" "Haramun ne, babu kyau ai." "Good." Ya fada har lokacin idon sa na kanta,kin dagowa tayi sarai ta gane da ita yake da kuma dalilin yin maganar. "Yo mu a zamanin mu ma ina muka isa? Kaya ne za'a yi maka su zani da riga da mayafi duk na atamfa, dinkin manya-manya haka muke sasu kuma." "Bari na kunna miki kallo Yaya." Tace tana son dauke maganar, tayi saurin chanja channel din zuwa arewa24 aka ci sa'a kuwa ana favourite film din Yayan, sai ta maida hankalin ta kan kallon ta manta da batun da ake magana akai.   Mikewa yayi hannun sa zube a aljihun sa, yace ta kawo masa abincin sa daki ya shige ciki, kallon Yaya tayi taga itama kallon ta take, a hankali murya k'asa k'asa tace "Sai kin koyi jan aji fa, kina kai masa ki dawo nan." "Toh Yaya." "Yawwa yi maza, dan naga kanki rawa yake ke dadi miji, masu irin halin Malam baa musu irin wannan rawar kan " Jidda na jinta ita dai tayi gaba zuwa kitchen ta hado abinda zata hado ta zo ta wuce ta shiga ciki, baya dakin ta dai ji motsin ruwa a toilet sai kawai ta ajiye masa ta fice kafin ya fito ya tsaida ta har Yaya taga ta dade. Tana komawa Yaya ta kalle ta "A kofa kika ajiye masa abincin Hala?" "A ah na kai har ciki." "Amma ko sakwan biyu fa bana jin kinyi." "Ba kince kar na dade ba." "Eh amma ai ba ina nufin kina shiga ki fito ba." "Hajiya Yaya, bari na koma toh." "Ban ce ba, karo min naman nan." "Toh." Ta kara mata ta zauna suna hira, tana fada mata yadda take so tayi bata son rawar kai, dariya kawai jiddah take dan tasan halin Yaya anjima k'adan sai ta chanja zance shiyasa ma take biye mata a duk yadda tazo. Bayan la'asar driver yazo daukar ta, har lokacin Tariq ko lekowa be sake ba, shiga Jidda tayi dan ta fada masa, ta same shi yana bacci, baccin la'asar da bashi da amfani, har gaban gadon ta karasa tana kallon fuskar sa, dan jim tayi a tsaye kafin ta juya da nufin barin dakin ya riko hannun ta, ta juyo da sauri still idanun sa na rufe har lokacin, "Mene kike kallo na." "Na'am? Ni?" "Am dama Yaya ce zata tafi shine nazo zan fada maka naga kana bacci shine zan fita." Fuzgo ta yayi ta fado kan gadon, ya gyara mata kusa dashi yana kallon fuskar ta, runtse idon ta tayi taki yarda ta bud'e, murmushi yayi ya matse mata hannun da ya rike tayi saurin bud'e idon ta, "Yanzu ma a hakan zaki sake fita wajen?" Ya rike gefen rigar jikin ta, da sauri ta girgiza kanta "Ba zan sake ba, dan Allah kayi hakuri Yaya na jira na." "Ba zaki fita ba toh." Waro ido tayi da sauri "Dan Allah kayi hakuri, wallahi tace kar na dade." "Ni kuma mijinki nace ba zaki fita ba, itama in banda abinda menene na zuwa gidan newly weds, idan ta gaji zata tafi gobe ba zata dawo ba." "Na shiga uku, ka rufa min asiri dan Allah." "I'm serious, ba in da zaki." "Na shiga uku, Amma..." Hannu yasa ya rufe mata bakin ta, tayi tsit tana zaro ido, shafa lips dinta ya shiga yi a hankali yana zagaya hannun sa akan dan karamin bakin nata. "Kina sake magana I ll kiss you." Rufe idon ta, tayi kirjin ta na bugawa da sauri da sauri, ta rasa dalilin da yasa yake mata haka, kallon ta ya cigaba da yi bashi da niyyar kyale ta, kuma yana sane sarai yasan shikenan sun tabo Yaya, zai so yaga yadda drama zata kare dan yau sai ta kusan kasa bacci akan hakan. Shiru ne ya biyo bayan maganar da yayi, ta dan bud'e idon ta kad'an taga ya rufo da kansa saman fuskar ta, so close da ko yaya ta sake motsawa fuskar ta zata taba tasa, juyar da kanta tayi dayan barin da nufin tayi magana "Dan Allah..." Ai bata karasa ba ya tallafo fuskar ta da hannayen sa biyu ya juyo da fuskar ta yana hade bakin su waje daya. Shiru shiru babu jiddah babu alamar ta, dan daga murya Yayan tayi ta kira sunan ta amma shiru, kama baki tayi cike da mamakin Jiddan, wato itama A ce tana mata kallon sum-sum ashe munafuka ce irin Tariq din, kwafa tayi ta fita fice tun a mota ta fara yiwa Isyaku da Sam mita, su dai jin ta kawai suke Isyaku yana bata hakuri ya samu suka kaita gida sannan ta kyale su. A compound din suka hadu da Fauwaz aikuwa ta fara fada masa wulakancin da Jidda da Tariq sukayi mata dan taje gidan su "Ashe Jiddan ma munafuka ce ban sani ba? Ta koyi halin mijin nata ni zasu wulakanta?" "Ai kema Yaya ban da abinki, ai ba'a zuwa gidan sabon aure yanzu, ba irin Malam dinki bane na zamanin dah, dan ma Ya Tariq din ne idan nine da police dog zan hada ki su rarakamin ke." "Sai dai su raraka ubanka bani ba, bakin mugu." "Allah kuwa, zuwa zaki ki hana mu shan soyayyar mu." "Idan kunga dama ku cinye juna tsabar soyayya, kuma ba gidan Tariq ba ma babu wanda zai sake zuwa gidan sa a cikin ku bare ku cimin mutunci, ba dai akwai ciki da goyo ba, muna nan zaku zo har in da nake." "Allah ma kar yasa muzo rokon abu wajen ki Yaya, wallahi dan zaki wulakanci ba dan kad'an ba." "Zaka maimaita wannan maganar, kuma ko kafarka na sake gani a gida na sai ka gane baka da wayo." Tayi gaba shi kuma ya cigaba da kyalkyala dariyar da yake, sosai ta shaki abinda Fauwaz din yai mata ga mamakin Jiddah, duk sai ta kasa zaune ta kasa tsaye ta dinga mita ita kadai. ***Sakin ta yayi bayan yaji tashin motar su Yayan, juyar da fuskar ta tayi haushin kanta da kunyar Yaya na kamata, toh da wanne ido ma zata kalli Yaya yanzu? Me yasa duk abinda ya fada akanta ta kasa dake masa a duk sanda irin haka ta faru sai ta bada kai bori ya hau, daga baya kuma tazo tana jin haushin kanta. Da kunnenta taji yana cewa ita ba spec dinshi bace ba, amma kuma why? Maganganun da ya fada ranar da ya fara dawowa, da wanda ya maimaita daga baya ne suka shiga dawo mata daki -daki, mikewa tayi tana bata fuskar ta, ya bita da kallo ganin yadda ta sauya lokaci daya "Menene?" Yace yana zuro kafafun sa ya sakko daga gadon "Ka bari idan ka samu spec dinka sai kayi yadda kake so,ni ba type dinka bace ba." "Jidda?" Yace yana mikewa, sake bata fuskar ta tayi sosai dan ma kar ya samu dama akanta, "Me kike son cewa?" "Nace ni Jidda ba type dinka bace, ka samo daidai da kai ni nayi maka siranta da yawa, kuma maganar aure ba zata taba yiwuwa a tsakanin mu ba." "Subhallah, me ya faru? Why are you saying all this?" "Abinda kace kawai nake maimaitawa, please ka kyale ni ka samu daidai da kai." Kallon cikin idon ta yayi, be hango komai ba sai iya gaskiyar ta akan maganar da take yi, yana tsaye ya rasa abinda zai ce dan be yi tunanin taji duk abinda yace wa Fauwaz ba, be rikice ba a zahiri sai dai a badini wani irin tsoro ne ya shige shi, ya shiga takowa zuwa in da take a tsaye, da sauri ta tura kanta ta fice daga dakin, ta nufi dakin ta ta shige ta rufe da mukulli. Tsayawa yayi a falon yana kallon kofar da ta shiga, ya dade a tsaye sai ya juya ya samu kujera ya zauna yana jiran fitowar ta. Dama wajen goshin magriba ba ne, saboda haka yayi alwala a toilet din falon ya sake tsayawa ko zata bud'e amma har akayi kiran sallah bata bude ba, masallaci ya wuce ana idar da sallar ya sake dawowa amma still dakin a rufe yake, gashi be san ta in da zai fara yi mata knocking yace ta bud'e ba. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (42 Mota ya koma ya dauko bakin glass dinsa ya saka sannan ya shiga wajen Yayan, share shi tayi har ya zauna yana kallon ta, ta cikin glass din yana so yayi dariyar yadda ta turbune fuska ta kautar da kanta a dole ba zata kalle shi ba "Ina kwana?" Shiru "Yaya ina kwana?" Nan ma shiru kamar ba da ita yake ba, waka ta fara tana karkada kanta tana habaici abinda ya bashi dariya yayi k'adan yana mikewa "Tunda ba zaki kulani ba bari na tafi." "Da uban me ya kawo ka? Ko ka nuna min ku tantirai ne kaida Jiddan?" "Me mukayi?" "Oho, duk abinda ma mutum yayi dan kansa." "Kizo mu tafi ki bini toh." "Idan na bika ba suna na Hadiza ba kenan, ni da gidanku ai har Abada, Allah ya taimaka ya bada sa'a." "Toh kiyi hakuri kinji?" "Ni kyale ni, sum-sum dakai kamar mutumin arziki, har ita Jiddan ashe itama munafuka ce, za tazo har in da nake ne." "Kunfi kusa." Yace yana mikewa "Sai kinzo Yaya." Ya zura hannayen sa cikin aljihu ya fice, ya nufi wajen masu gadi ya zauna yana sauraron hirar da suke duk da be saka musu baki ba, hakan ba karamin dadi yake musu ba, sam yaran gidan kaf basu da girman kai ko kadan haka ma fauwaz da yafi Tariq din magana yake zama dasu har suyi hira sosai. Ana haka shima Fauwaz ya dawo ya sameshi a wajen zai zauna yace su je ciki. Tashi yayi yabi bayan sa suka jera yana tambayar sa karfe nawa su Baba suka tashi. Suna shiga ciki ya kama hannun Fauwaz din ya murde shi ya baya, ya fara ihu "Washhh!!! Da zafi fa." "Me yasa mukayi magana kaje ka fadawa J..." "J?" "Jidda." "Oh wacce magana?" "Maganar da mukayi ranar da na dawo, how comes ta sani idan ba fada mata kayi ba." "Oh tab! Ai tana tsaye time din tazo kawo maka ruwa da juice taji komai." "Shit." Ya sake shi yana dunkule hannun sa "Me ya faru?" "She's punishing me." "Kamr yaaya?" "Tace na kyale ta, naje na nemo type dina, and since then ta daina kulani." "She's right, shine zaifi sauki." "But ai da ba haka take acting ba, tana min magana ko da kadan ne, yanzu fa ko kallona batayi, kaamar ma ta tsane ni." "Abun ya dameka sosai?" "Sosai, yadda baka tunani, I'm thinking of not going again, bansan idan na tafi ko zata ce ta fasa ba." "Then kayi mata bayani." "Na me?" "Kace mata mistake ne ba abinda kake nufi ba, ka fada mata you want her so bad baka so ka rasata, da dai irin wannan stuffs din, ka dai gane." "Wa ni? Noo ba zan iya ba, kawai dai bana so ta daina min magana, amma ni ba zan iya karya ba." "Karya?" "Ehen, na fadi abinda nasan ba haka bane." "Tirkashi, then ka kyaleta kawai, tana da every right da zatayi fushi ta daina kulaka, let her be, zan mata magana idan Baba yazo sai ta same shi nasan zai fahimce ta, kai kuma sai ka samo type dinka, a think hakan yayi." "Idan ka fada mata haka wallahi zan iya fasa bakin ka, ni ba haka nace maka ba,I just need a solution ne kawai." "Toh Ya Tariq ya za'a yi? Baka son ta, she's not your type, dan babu bukatar cigaba a zaman ku tare, free her Dan Allah, nasan zata samu..." Ai be kai karshe ba yaji ya bige bakin sa, ransa a bace ya balbale shi da masifa, kar ya ya sake ya kuma sako maganar wani, sai da ya gama sannan Fauwaz din yace "Kayi tunani dai, if not zaka rasa Jidda." "Idan Mama ta dawo kace mata nazo, I'm going." "Ok." Juyawa yayi ya fita shi kuma Fauwaz ya zauna yana mamakin ace wai Ya Tariq din ba zai iya gane halin da yake ciki da kansa akan jidda ba, ko kuma dai ya gane kawai dai tsabar ki fadi ne be sani ba, shafa bakin sa yayi Allah yaso be fasa masa shi ba a garin kishi dan yau zai je wajen Hidaya da yamma. Da hannu daya yake tuki dayan yana danna counter kansa a gaba yana kallon titin da yake dauke da tsirarin ababen hawa, gida ya nufa tunda ya baro gidan su yayi zaman sa a central mosque sai da akayi magriba sannan ya nufi gidan kansa cike taf da maganar Fauwaz da ya wuni yana bitar ta ya kasa gano in da ya kuskure, a tunanin sa baya bukatar ya bude baki ya fad'awa Jidda komai, ba kuma ya jin zai iya nan kusa amma kuma ya kamata ace ta masa uzuri ta gane yadda ya damu da ita sosai, sau wajn goma a yinin ranar yana gwada kiran wayarta sai tayi kamar zata shiga sai ya katse yana maimaitawa kansa babu amfanin kiran. Horn yayi Yahaya ya taso da gudu ya bud'e get din ya shigo yayi parking sannan ya fito ya jefawa Faisal key din, ya gaji da tuki ba zai sake ba har sai ya dawo, Kano zasu je jibi kuma a jirgi zasu duk abinda zai taso ma a cikin garin Faisal din ne kawai zai kaishi "Akwai baki a gidan ne?" "Eh Amira ce da wata." "Ok." Yace yana yin gaba, sai kuma ya juyo "Ka zama a kusa ko yaushe zan iya kiran ka, a wanke black car din chan da ita zan fita gobe in sha Allah." "Ok sir, an gama." Haurawa yayi zuwa kofar da zata sadaka da cikin gidan ya sa key ya bud'e, suna zaune su uku a falon Jidda da Amira na zaune a kujera daya sai Salma dake kwance tana danna waya, da sauri ta tashi zaune tana gyara zaman ta, riga da skirt ne a jikin ta da suka dan kamata babu ko mayafi, tunda tazo uffan bata cewa Jiddan ba, itama bata kulata ba suna ta hirar su da Amira har Ya Safiyya ta kira Amiran tace ta bawa Jiddan ta tashi daga wajen taje sukayi wayar ta dawo ba tare da sun ji me suka tattauna ba. Mikewa tayi tana fadada fara'ar fuskar ta, ta nufe shi daga in da yake tsaye yana zare takalmin kafarsa daga tsaye, kallon ta yake tana karasowa har tazo daf dashi, ta dan russuna kad'an tace "Sannu da zuwa." Fuskarta dauke da murmushi, murmushiin ya maida mata yace "Thank you." Yana mika mata hannun shi, dan noke kafadar ta tayi ta mika masa hannun a kunyace duk nauyin shi da su Amira dake zaune a wajen na cikata, amma dole tayi bayan wayar sa sukayi da Ya Safiyya dan ba zata taba bari Salma ta samu galaba akanta ba. Idon sa akan lips dinta da yasha jan janbaki me kyau da sheki, kamshin turaren da tayi amfani ya cika ko ina ya sashi a wani yanayi. Hannun ta sarke da nasa suka karasa shigowa tsakiyar falon "Ya T... welcome." Salma tace haushin Jiddan da abinda ta aikata na tike ta "Yawwa." Yace yana kallon Amira da kunyar zuwan musu gida duk ta cikata "Welcome Yah." "Kece munafuka ko?" Yace yana hararar ta "Allah Ya ba ruwana wallahi." "Naji." Yace suka wuce zuwa kofar da zata kaisu dayan falon, yasa hannu ya bud'e musu ska shiga, suna shiga tayi saurin janyewa tana kin kallon sa, tsayawa yayi saroro yana duban ta, dakin ta, ta shige ta barshi a tsaye a wajen cike da mamakin ta! *_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_* _(Where every flavour tells a story .....)_ *_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_ _08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_ _INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*? GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_ _MU NA YIN:_ *_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_* *_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_* *_LOCAL DRINKS:_* _HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_ _MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._ _KADA KU MANTA MUNA YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._ _FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_ _ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_ _PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_ *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (41) ***Ya dade a zaune a falon dan anan ya kusa cinye fiye da rabin daren sa hoping ko zata bud'e amma har ya gaji ya tashi ya shiga ciki ya gyara pillows din dake kan doguwar kujera dake dakin ya kwana dan baya jin hawa gadon. Juye -juye ya dinga yi yana tunanin maganganun, ya fadi dukka kuma ko kad'an yasan be kyauta ba, ya yi kuma dana sanin furtasu duk da be yi tunanin Fauwaz zai fada mata ba, tunda shi dai ba a gabanta yayi waccar magaanar ta farko ba, ko shine dole yaji babu dadi ita ta ma yi hakuri sosai. Kunya ce ta lullube shi tunawa da yadda ya gama cika baki kuma yazo yana kissing din yarinyar mutane bayan ta san duk abinda yace a kanta. Fauwaz ne ya cuce shi tunda dai da be fada mata ba fuskewa kawai zai yi duk da ya taba fada taji ya san kuma taji din amma maganar bata kai munin wannan din ba. Da wuri ya tashi bayan ya samu yayi baccin kad'an, ya fito falon ya zauna sanye da jallabiya me gajeran hannu yana jiran fitowar ta. Bayan kusan awa daya da zaman sa sannan yaji ana murd'a key din dakin, yayi saurin dauke kansa daga kallon dakin ta fito fuskar ta a gaba bata ko kalli bangaren da yake ba, ta fice zuwa dayan falon na farko in da ta shiga kitchen ta duba abinda zata duba ta dora ruwan tea, falon ya dawo ya zauna idon sa na kan kitchen din yana jin motsin ta, ya kunna TV pretending kaamar yana kallo ne amma rabin hankalin sa yana wajenta. Godiya taje ta kirawo tazo ta tayata ta soya musu doya da egg sauce ta dafa ruwan tea me kayan kamshi ta jera akan saman Iceland din ta zuba ma Godiya nata tace taje taci sai tazo ta gyara kitchen din. Karba tayi ta fita daga kitchen din ita kuma ta d'aga cikin wajen oven din zata saka ragowar man da tayi amfani dashi ya shigo ya tsaya daga jikin island din yayi folding hannuwansa a kirjinsa yana kallon bayan ta. Dagowa tayi ta juyo ta ganshi tayi saurin dauke kanta ta dau plate din da ta zuba nata rike da cup tazo zata wuce shi. Saurin tare hanyar yayi ta dan ja baya da sauri "Goodmorning tunda baki iya gaisuwa ba." "Ina kwana?" Tace a gajarce ta nuna masa hanyar "Zan wuce." "Fushi kike dani?" Girgiza kanta tayi, "Ni ba fushi nake ba." "Toh menene, kika chanja all of a sudden." "Ba komai, zan wuce." "Ba in da zaki, sai kin fada min." Ajiye abun hannun ta tayi a gefen Iceland din ta wuce gaban sink ta soma wanke kayan da suka bata da ta barwa Godiya ta wanke. Jan daya daga cikin kujerun dake jikin Iceland din yayi,ya zauna ya soma cin doyar daga cikin plate din da ta ajiye a gefen yana shan tea din yana kallon ta, sai da ta gama tatas ya goge hannun ta, ta fice daga kitchen din ba tare da ya sake tsaida ta ba, ya kuma cinye mata abincin da ta zuba duk dan tayi masa magana amma sai ta nuna kamar ma bata san me yayi. A rayuwar sa ya tsani silent treatment duk da shi yafi kaurin suna a wannan bangaren amma ya tsani wani yayi masa sai yaji kamar kansa zai yi bursting, ta gwammace ta zauna bata ci komai ba akan ta yi masa magana kenan. Ransa ne ya dan sosu, a kalla yayi kokari har yake bin ta tana botsarewa bayan be taba hakan ba, zai gwada kyaleta yaga iya gudun ruwan ta. Wanka ya shiga ya shirya ya fito yana daura links a jikin hannun rigar sa Mama ta kirashi tace Amira zasu zo da Salma gidan su kwana biyu, wani banbarakwai yaji har ya kasa hakuri yace; "Kwana Mama?" "Eh kwana, ko kar suzo?" " A'ah, amma..." "Mahaifin ku shi kadai kake ma biyayya Tariq, ba zan ce kayi min ba, ba kuma zan hana ba, shikenan ba komai." "A ah, i'm sorry, kiyi hakuri,sai sunzo." "Shikenan, yaushe zaka tafi?" "Nan da kwana hudu ko in sha Allah." "Ok sai su zauna har sai ka dawo." "Toh Mama." Hula ya saka bayan ya gama wayar ya fice daga gidan a tunanin sa hakan sai sa ya manta da ita da tunanin abinda ya addabi zuciyar sa. Kai tsaye gidansu ya nufa dan so yake ya samu Fauwaz yaji yadda akayi ya fada mata maganar da sukayi sannan ya samu Hajiya Yaya. Sabani sukayi da Fauwaz din yana fita shi kuma ya na shiga gidan. Wajen aunty ya fara zuwa ya gaishe ta sannan yace yana so ayi Jidda lefe kamar yadda akayi wa kowa, mamaki ya bawa Aunty amma a k'asan zuciyar ta dadi take ji, ya soma siyan wasu kayan online amma wasu dai zai bar Auntyn ta siyo. A haka suka rabu ya nufi wajen Mama, bata nan ta fita sai Aunty Nafi da su Amira dake shirin tafiya gidansa wanda ba asan ran Amira zaa baka dan dai tana shakkar Mama ne sannan kuma ba zata bar Salma taje ita kadai ba dan tasan dalilin zuwan ba na Allah da annabi bane, so take ma ta fadawa Ya Fauwaz yasan yadda zai sanar da Ya Tariq din ko Mama ta kirashi kar ya yarda amma sai ji tayi suna waya da Maman kamar ma kuma har ya amince. A tsaitsaye ya gaida Aunty Nafin da wasu mata su biyu ya fice yana jin tana maganar ya tsaya Salma ta kawo masa breakfast amma yayi biris ya ja dan siririn tsaki dan baya son yadda matar take masa sam, ya kuma lura ita ke zuga Mama dan dazu ya jiyo sautin muryar ta,tana cewa Maman kar ta raga masa idan yaki amincewa kawai sharewa yayi amma ya jita, baya son munafukan mata kuma sai yasan yadda yayi yasa ta tarkata inata tayi gaba dan ba zai iya tolerating dinta ba. *_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_* _(Where every flavour tells a story .....)_ *_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_ _08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_ _INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*? GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_ _MU NA YIN:_ *_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_* *_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_* *_LOCAL DRINKS:_* _HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_ _MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._ _KADA KU MANTA MUNA YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._ _FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_ _ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_ _PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_ *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (43) ***Kad'a kansa yayi zuwa ciki ya rage kayan jikin sa, ya shiga ya watsa ruwa ya fito, ya saka gajeran wando da bakar t-shirt ya nufi dakin nata. Murd'a kofar yayi ya shiga da sallama a ciki sosai. Tana tsaye gaban mirror fuskar ta da ruwa alamun alwala tayi. Takawa ya shiga yi har zuwa daf da bayan ta, suka hada ido ta cikin mirror din ta turo baki tana kokarin barin wajen ya riko ta, ta baya ya zura hannuwan sa ta, ta tsakanin cikinta ya rungume ta a tsakanin chest dinsa. "Me nayi miki?" Yayi maganar a cikin kunnenta, ta dan ya mutse fuska ta kauda kanta, jawota ya yi da baya da baya har zuwa wajen gadon still yana rike da ita ya zauna yana mata masauki a saman cinyar sa sannan ya sake riketa gam yadda ba zata tashi ba "Sai kin fada min, me nayi kike share ni?" "Ba komai." "Ba wani, fada min naji." "Sallah zanyi fa!" "Sai kin fada min zan kyale ki, ba wani wayo da zaki min irin na ranar." "Ni ba komai, please ka kyale ni." "Ba zan kyale din ba, kuma kika kara kwakkwaran motsi sai na baki mamaki, kinsan kuma gidan ba mu kadai bane." Shiru tayi ta daina kokarin tashi din dan bata san me zai mata ba, wata irin kasala yake ji hade da wani irin yanayi me wahalar fassarawa, rike ta ya sake yi sosai a jikinsa yana shakar kamshin turaren jikinta da be taba jin irin sa ba.    Harhada kalaman da zai fada mata ya shiga yi a zuciyar sa, ya rasa exact words din da zai yi amfani yace mata abinda taji ba gaskiya bane ba, matsala aka samu, amma kuma ta yaya? Baya so ya karyata kansa da kansa ko yace mata be fada ba bayan tasan komai, hakuri zai bata toh? Ko cewa zai Jiddah ina sonki? Da sauri ya hau girgiza kai, gwara ma ya bata hakurin kawai. Gyaran murya yayi ta dan motsa kad'an ya sake riketa "I'm sorry toh." "For?" "Komai ma, duk abinda nayi miki na sanshi ko ban sani ba kiyi hakuri kawai." "Kuma dole ki hakura ma, tunda na baki hakuri." Ya dora yana sake jaddadawa kansa yayi daidai abinda yace. Murmushi ta samu kanta da yi, be ma san takamaimai yadda zaiyi ya bata hakurin ba, be saba ba ko kuma dai tsabar ego dinsa ne ba zai barshi ba, dole zata kara jan ajin ta sosai tunda yanzu ta gama gano yadda ta yi tasiri sosai a cikin rayuwar sa. "Kinjiiiii ?" Ya ja maganar jin bata ce komai ba, girgiza kanta tayi tace "It's not enough, ni ban hakura ba." "Gosh! Why? Mesa? Ki hakura mana kawai." "A ah, ban hakura ba, zan tashi nayi sallah pleaseeee, zan koma wajen su Amira kuma." "Wallahi baki isa ba, ba in da zaki. Yar karamar yarinya dake kina bani headache, ba na baki hakuri ba, mistake ne ba haka nake nufi ba, ba zan sake ba kuma." "Toh zan yi sallah." "Naji, naji." Ya saketa ta tashi, ya mike a tunanin ta fita zai sai kawai taga ya saka key a kofar ya cire key din ya dawo ya haye gadon ya kwanta rigingine. Bata ce masa komai ba, ta koma toilet ta sake wata alwalar sannan tazo ta tada sallah yana kallon ta, ta idar ta mike ta cire Hijab din ta maida shi cikin wardrobe dinta ta, ta dauki rigar baccin ta milk colour da wani khumra me shegen kamshi ta shiga toilet din ta chanja ta shafa turaren a dukka gabobin dake jikin ta har da k'asan guiwar ta kamar yadda Ya Safiyya tace mata sannan ta fito, ta maida su wajen da ta dauka tazo ta dayan side din ta dauki wayarta akan drawer ta zauna daga gefen gadon tana dannawa. Kamshin turaren ne ya dinga shigar masa hanci ya chakude da wani mixed feelings da ba zai iya resisting ba, mikewa yayi ya zauna sannan yace "Come here." Kamar bata ji shi ba, ta cigaba da danna wayar gabanta na faduwa saboda yadda taji muryar sa very deep. "Jiddaaaaa..." "Um?" Ta waigo ya nuna mata kusa dashi "Zo nan" Dan jim tayi tsoron ta na daduwa sosai, tasowa tayi tana jan kafa tazo gabansa ta tsaya tana kallon kasa, daidaita kansa yayi yana sauke ajiyar zuciya bayan ta zauna a gefen sa kafafunta na kasa. Matsowa yayi ta bayan ta, ya sakata a tsakiyar kafafunsa ya dora kansa a gadon bayan ta. "Waye yabaki hint akai na? Fauwaz? Safiyya? Ko wa?" "Naa..mm?" "Fada min, nasan dole a cikin su ne, so suke na zauce ko? Shine suka saki kike dagula min lissafi." "Ni ba kowa." "Ba wani, I can read your mind, nasan sune I have no doubt, munafukan yara." Dariya tayi yayi murmushi shima, yana feeling so comfortable da suke tare, "Tafiya zanyi." "Tafiya?" Tace "Eh, zan koma in da na fito." Shiru tayi ta tafi tunani, tafiya zai kenan ya sake barin ta? Ko zuwa zai ya dawo? Ji tayi duk babu dadi amma ta kasa cewa komai, jin tayi shiru yasa shi cewa "Ko bakya so na tafi?" "Ummm, bana so." "Me yasa?" "Ba komai." "Dole akwai dalili, tell me, idan naji dalilin babba ne zan fasa kwata-kwata, nayi zamana anan watching you all day long." Ya karasa maganar a ciki ciki yadda ba zata ji ba "Zaka dade ne ?" " Eh, kamar shekara daya haka." Ya tsokane ta Dauke wuta tayi gaba daya, ta tuna Yasmin, zuciyar ta,ta fara raya mata abubuwa masu yawan gaske, juyo ta yayi da hannun sa ta dawo tana kallon shi, sai yaga gaba daya ta nuna damuwa a fuskar ta, walwalar ta ta ragu sosai "Tell me, bani reason me karfin gaske, da zan fasa na zauna anan." "Nasan ba zaka fasa ba, bansan kuma me zaka je kayi a chan din ba, Allah ya kiyaye ya dawo da kai lafiya." "Zaki bini?" Ya samu kansa da tambayar ta, shiru tayi bata ce komai ba, ya dinga kallon ta kamar ranar ya fara ganin ta, hugging dinta kawai yayi a kalla hakan zai sa ya samu saukin bugawar da zuciyar sa takeyi da karfi wanda har yake tunanin zata iya ji. "I love you Jidda." Ya furta a chan k'asan makoshin sa, wanda ya shiga har cikin kwakwalwar ta ya zagaye ilahirin jini da bargon ta, ji tayi kamar ana zare mata kasusuwan jikin ta, ta runtse idon yar karamar kwalla ta biyo gefen fuskar ta, be san taji ba, a tunanin sa ba zata ji maganar da yayi ba, shiyasa be kawo komai ba, bata nuna masa taji ba, ta yi luf yana shakar kamshin jikinsa da ya kasance ya kama jikin a ko da yaushe kamshin yake yi. Sun dade a haka, shi ya fara zare jikinsa yana gyara mata zama a sosai a jikin sa, tayi luf kamar mage, a duk lokacin da ta ji ta a jikin shi sai taji gaba daya komai na duniyar ya tsaya chak, bata ji da tunanin kowa sai duniyar su, me dauke da iya su biyu kawai. Hannun sa a saman gashin ta, yana shafawa a hankali har bacci ya soma fizgarta, yana ganin sanda take rufe idon ta, sai ya sake gyara mata kwanciyar sosai yadda zata ji dadin yin baccin ba tare da takura ba. A zaune ya soma baccin shima dan baya so ya motsa ya katse mata baccin ta, sai chan dare ya janye ta ya kwanta shima yana sakata a jikinsa yayi mata rumfa da jikinsa. Ran Salma ya kai kololuwa a baci amma sanin Amira ba zata biye mata ba yasa bata ce komai ba, ace dan wulakanci tunda ta shige bata saka fitowa ba, ko sai da safe ai ta ce musu, gashi babu damar bin bayan su amma dole ta kira mamin ta gobe ta fada mata Ya Tariq din yana son Jidda dan ko makaho zai iya tantancewa tsananin son da yake mata a yan sakanni da basu wuce biyar ba, bata san Jiddan ma A bace sai da taga ta kama hannun Ya Tariq din ba kunya sun yi shigewar su, ita duk kallon wawiya yar kauye take mata duk da wayewar da tayi amma ta raina ta sosai, sai gashi tayi abinda ya bata mamaki ya kuma daure mata kai dan Ya Tariq din ma bata taba kawo zai iya yin abinda yayi jiyan ba, su Mama bonono suke wato rufe kofa da barawo, a tunanin su ba zai taba son Jiddan ba sai gashi zata basu mamaki. Tana kallon Amira tana jan munshari amma ita ta kasa tana tunanin me yake wakana a chan wajen su, son Ya Tariq din take da mugun kishin sa, dan tun ba yau ba Anty Nafi take kwadaita mata auren Tariq din shiyasa duk tabi ta gama tsara rayuwar ta, da yadda take so ta kasance, ko wannan gidan da suke ciki a buri da hasashen ta yayi mata mugun kad'an gida take so na alfarma na kece raini da ma'aikata birjik suna mata hidima ta huta sosai taji dadin rayuwar ta. Ta dade tana wannan lissafin wasikar jakin kafin ta samu bacci ya dauke ta mara dadi. Amira ce ta rigata tashi ta riga su dukka ma tashi dan har su Jiddan basu fito ba a daki Ya Tariq din ma yayi sallar asubah shi da Jiddan suka koma suka kwanta duk da nokewar da take tana jin kunya amma yaki barin ta, dole ta kwanta tana zara ido ya kanainaye ta da hannayen sa ko kwakkwaran motsi tayi a jikin sa zatayi shi. Godiya taje ta taso tazo ta gyara falon tas tayi moping Amiran na guiding dinta ta dauko turaren wuta ta saka a burner nan da nan gidan ya dau kamshi ta koma daki tayi wanka ta fito kenan Salman ta tashi daga baccin wanda bata jin ko sallar asubah tayi tana bacci, mika tayi tana kallon Amiran da ita ma kallon ta take "Kinyi sallah kuwa?" "Yanzu zan yi." Ta sakko daga gadon ta dauki towel din da Amira tayi amfani dashi ta shige toilet din, tsaki Amiran tayi dan bata son sharing da kazanta kuma akan towel din kusan sau uku suna fada amma taki daina dauka. Cigaba da shiryawa tayi tana cikin shiryawar Jidda ta kwankwaso ta shigo ciki ta zauna a gefen gadon tana kallon yadda gadon ya hargitse. "Goodmorning Matar Yah." "Kina da matsala, ina Salma?" "Ta shiga toilet,jiya shine kika gudu kika barmu." "Bacci nayi da wuri shiyasa, " "Fadi gaskiya dai, ko dai Ya Tariq ya hanaki dawowa?" "Eh shine ya hanani, tunda haka kike so kiji." "Good, a cigaba da rikita min yayana, I trust you." Dariya Jiddan tayi, Salma dake tsaye jikin kofar toilet din taki fitowa ko zasu fadi wani abun ta samu dorawar sai taji tace "Kunyi breakfast kuwa?" "A ah, amma aunty ta kira a wayar ki dake falo, dan har zan sama mana wani abun sai kuma ta kira na dauka tace Sam ya taho." "Yawwa, na huta bari na kirata." Ta mike ta fita, sannan Salma ta fito, Amira ta kalleta ta tabe baki ta dau wayar ta. Zuwa tayi ta kira Aunty tana dauka ta fara fada "Amira da Salma a gidan nan suka kwana wai?" "Ya Aunty, jiya suka zo." "Jiya? Ina Tariq din? Me zai sa su kwana a gidanku?" "Zuwa kawai sukayi Aunty." "Karya ne, turo su akayi wallahi, wannan wane irin abu ne, kina ji na, karki yarda ki yi sake ki saki mijinki har su samu dama akanki, yarinyar nan Salma ba dan Allah aka turo ta ba, idan kika tsaya shashanci sai ta raba ki da gidanki." "Aunty, waye zai turo ta? Kuma tayi me?" "Ta kashe miiki aure mana." Zaro ido tayi, "Ni? Akan me yasa?" "Oho, karki tsaya tambaya kiyi abinda ya dace, kuma bari, dani suke zancen wallahi na daina kyalewa, Yaya zan fadawa wallahi." "Aunty dan Allah ki daina shiga matsala akai na." "Ba wata matsala, na daina kyalewa kawai." Fitowa yayi sai tayi shiru tana sauraron Auntyn, a gefen ta ya zauna sai tayi saurin cew "Shikenan aunty, sai yazo." Ta kashe ta ajiye wayar a gefe, "Sam ne zai kawo mana breakfast in ji Aunty?" Gid'a kansa yayi yace "Ni nake nake so." "Nawa?" "Um... Golden morn zan sha." "Ok,." Ta mike ta nufi kitchen din, ta shiga taga ko ina an gyara tsaf, tasan da tainakon Amira dan amira sam bata da son jiki ko kad'an, bud'e cabinet din da tarkacen kayan su madara suke ciki ta dauko golden morn din ta ajiye akan iceland ta dauko mug, motsi taji a bayan ta ta juyo sai taga Salma ce ta shigo kitchen din, ta wuce kai tsaye wajen sink ba tare da tace komai ba, dauke kai Jidda tayi dan bata isa itama ta kula ta ba, musamman bayan aunty ta fada mata dalilin dayasa aka turo ta, cup ta dauka ta dauraye a sink din sannan tazo gefen ta, ta bud'e ta dauko kayan tea ta zuba a cup din tana had'awa. Fita jidda tayi bayan ta dora komai akan dan madaidacin tray ta wuce daki dan ya bar falon, ta kai masa sai ta tuna babu ruwa a fridge din cikin dakin ta dawo da nufin dauka, tana shiga tsantsi ya kwasheta, ta kwalla kara da karfi kafin ta zame gaba daya ta fadi a daidai kofar kitchen din. A guje ya fito Amira ma haka suka nufi kitchen din a rikice *_RANO SCRUMPTIOUS MEAL_* _(Where every flavour tells a story .....)_ *_By HAFSAT RANO_* _(Mother/wife/writer)_ _08030811300_ _IG:Rano_scrumptious_meal_ _INA MA'ABOTA ABINCI? WATO *TRADITIONAL FOOD IN KANO*?  GANGARIYAR ABINCI NA AL'ADUN HAUSA DA NAHIYAR KETARE? BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA. MUNA DA LEMUKA WATO *LOCAL DRINKS*. ZAKU IYA KAWO NA HIDIMOMIN LIYAAFA MUYI MUKU_ _MU NA YIN:_ *_FUNKASO_* *_ALKUBUS_* *_SINASIR_* *_WAINA_* *_ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI)_* *_COW TAIL/COW LEG (DAB'URI)_* *_CHICKEN AND FISH PEPPER SOUP_* *_LOCAL DRINKS:_* _HIBISCUS (ZOBO)_ _GINGER_ _AMAANI FRUITY SHAKE_ _MUN TANADAR MUKU MOUTHWATERING ABINCI KALA KALA WADANDA KE GINA JIKI DA KARA LAPIA. ABINCIN MU A TSAFTACE YAKE. KUMA MUNA YIN SU NE AKAN YADDA KOWANNE MUTUM ZAI IYA CI . AKWAI SPECIAL SOUPS NA MASU ULCER WADANDA BABU YAJI. AKWAI KUMA NA PEPPER DEM GANG GA MASU SON HOT AND SPICY...._ _KADA KU MANTA MUNA  YIN NA TAKEAWAY/ORDER . MUNA KUMA YIN NA BIKI (WE CARTER TO SMALL/LARGE EVENT...._ _FUNKASO TO PAIR WITH COW TAIL:2K_ _WITHOUT COW TAIL:1K_ _ALKUBUS TO PAIR WITH ASSORTED MEAT (KAYAN CIKI) 2K. WITHOUT ASSORTED MEAT :1K_ _PLS NB: PAYMENT VALIDATES INTEREST..... DELIVERY WITHIN KANO:500 NAIRA_ *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________*     *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_  350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350    *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350     *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350      *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350     *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350     *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_  *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: ._SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (45) ***Ruwa ya kawo mata ya taimaka mata ta sha ya ajiye yana hawa gadon. A hankali kukan da take ya dauke ya koma sai ajiyar zuciya da take saboda azabar da tasha, sanyi taji na ratsa ta, nan da nan ta soma rawar sanyi ya tashi ya kashe AC ya rage fan din, amma duk da haka bata daina ba, sosai zazzabin ya rafke ta wanda dama take ta jin alamun sa tun jiya amma ta daure sai gashi ya taso lokaci daya dalilin gyaran. "Jikinki yayi zafi sosai." Yace yana kama hannun rigar ya zare mata shi, da sauri ta kalle shi shima ita yake kallo, ya girgiza mata kansa ya karasa zare mata rigar baki daya, wani irin yarrr yaji tun daka kansa har zuwa tafin kafafunsa, ya ja ajiyar zuciya ya daure ya ja karamin blanket ya rufa mata a daidai cikin ta zuwa saman chest dinta, idon ta dake a runtse tunda ya janye rigar ta dan bud'e taga ya dauka daga kan gadon, ya cire rigar dake jikin sa har singlet din, saurin maida idon tayi ta rufe tana jin sa ya hawo hadon ya jawo ta jikinsa ya gyara mata kwanciyar, zafin da jikinta yayi ya hadu ya chakude da bare fatar sa. Wani irin yanayi suka samu kansu a ciki musamman shi, ji yayi baki daya duniyar na juya masa, komai ya tsaya chak hatta bugun zuciyar sa ya karu da kaso me yawan gaske. A hankali zazzabin ya dinga raguwa har ya zama sai dan dumi kad'an. "Gumi nake." Tace sai ya sassauta rikon da yayi mata amma ba dukka ba, kanta na jikin kirjin shi tana jin yadda bugun zuciyar sa ke tsere, zufa na cigaba da keto mata ga wata matsananciyar kunya da ta rufe ta, dan babu komai a saman ta sai bra wadda itama kusan rabin kirjinta a waje yake saboda yadda karfen dake rige ta ya zare garin cire zip din rigar. Ta kasa motsi ko kad'an dan ko yaya ta motsa chest dinta zai iya haduwa da jikin sa. "Are you feeling better?" Ya tambaya da k'yar bayan ya daure yayi maganar dan hatta yawun bakin sa ya dauke da k'yar ya nemo shi, be taba samun kansa a irin wannan yanayin ba, shiyasa duk ya kasa controling kansa, wani irin heavy feeling yake ji gashi baya so a samu matsala. Da ka ta amsa masa sai ya zare jikin sa a kasalance ya tashi yana kin kallon ta, duk da dama idonta a rufe yake ita, ya dauki rigar sa ya zura ya shige toilet, mikewa tayi da k'yar ta yi kokarin gyara maballin bra din amma ta kasa, tayi tayi sai kawai ta hakura jin zai fito ta koma ta kwanta tana sake kudundunewa da bargon. Fitowa yayi yana goge kansa da ya jike da ruwa, yana daure da bathrobe alamun wanka yayi, ta k'asan idon ta, take kallon shi ya shafa man sa sai kawai ya zura jallabiya bayan ya fesa turare. Fuskar sa fayau sai dan idonsa da ya dan yi ja kad'an da kansa da yayi masa wani irin nauyi na ban mamaki. Gefen ta ya zauna ya sakar mata murmushi bayan ta bud'e idonta, ya dauki wayar sa yaga text din ban hakuri daga Dr Sufyan da missed calls dinsa, kiran sa yayi ringing daya ya daga yana bashi hakuri "Ya hakuri captain, muna chan emergency unit wayar na batta anan Dr lounge." "Ba komai, dama nasan kila kana busy ne, ya aikin?" "Alhamdulillah wallahi." "Masha Allah, dama madam ce ta samu dan targade a kafarta, shine kuma sai zazzabi though da ban sameka ba daga gida an turo irin masu gyaran gargajiya din nan, sai kuma zazzabi daga baya." "Ayya Allah sarki, kaji tsautsayi, Allah ya bata lafiya, bari sai Dr Amina tazo ta duba ta, ina fatan dai ba aiki ka jikawa yar mutane ba, tsohon tuzuru." Da sauri Tariq ya kalle ta, yaga ta rufe idon ta, amma yasan taji me Sufyan din yace, murmushi yayi kawai yace "Sai dai tazo din, please tazo da wuri." "Ok shikenan, ka duba ta please." "In sha Allah, thank you." "DM." "Zaki yi wanka?" Ya tambaye ta bayan ya gama wayar. Da sauri ta girgiza kanta "Ina jin sanyi har yanzu." "Ok Dr Sufyan zai turo colleague dinsa ta duba ki, in sha Allah zaki ji dadin jikinki." "Thank you." "Shissh, get well soon kinji? Pleasee." Gid'a masa kai tayi ya mike ya fice tabi bayan sa da kallo sannan ta sauke ajiyar zuciya. Zama yayi a falon yana tunanin abinda ya faru a while ago, wani irin abu me kama da mayen karfe yaji yana fuzgarshi toward her, da ace kalou take yasan ba zai iya resisting ba, yanzu ma kawai managing kawai yake shiyasa ya fito ya barta dan zama waje dayan ba zai yi masa kyau ba, baya so ya kara mata akan wahalar da tasha da kuma wadda take ciki. Be taba tunani ko hasashen getting intimate with her ba sai yau, yau din ma yanzu amma duk da haka zai kara jira, zai jira right time din. Ba'a fi 30min da wayar ba Dr Amina ta karaso gidan ta hanyar amfani da address din da Tariq din ya turawa Sufyan din, a waje ta tsaya ta kira number Tariq din ya mike daga zaman da yayi daidai lokacin Salma ta fito ya kalle ta yayi gaba dan shigowa da ita. Fuskar sa a sake ya wuce mata gaba zuwa ciki ya nuna mata kujera ta zauna yace zai kirawo Jiddan, Salma na labe sai ta fito ta zauna a falon suka gaisa da Dr Aminan. Bacci ya sameta tana yi, ya rankwafa kanta ya dan taba ta a hankali, da yake baccin ba me nauyi bane sai ta bud'e idon ta, "Dr Amina tazo, zaki iya tashi?" "Eh." Ta daga kanta "Ok let me help you." Ya mika mata hannu sai ta noke kafada tunowa da tayi bata da riga, kallon ta yayi sai ya tuna "Ohh, tashi toh ki sa rigar zan jira ki a kofa." Ya juya mata bayan, tashi zaune tayi ta saka rigar a haka, ta tashi tana dosana kafar ta dauki Hijab ta saka ta taka a hankali ta same shi a tsaye, "Sannu." Yace yana kama hannun ta, suka fito hannun su sarke da juna. Hannun Salma ta kalla zuciyar ta, ta sosu taji kamar ta tashi ta ture Jiddan, da kansa ya taimaka mata ta zauna ya kuma zauna a gefen ta daf da ita har kusan rabin jikinta na nashi, murmushi Dr Amina tayi ta amsa gaisuwar Jiddan tace "Sannu amarya." Murmushi tayi shi kuma da tun fitowar su yaga Salma yace yana kallon ta "Ki tashi ki bamu waje, we need some privacy." "Eh?" "Kinji ai, excuse please." Tashi tayi wani kululun bakin ciki na tokare mata a makogwaro, ta wuce fuuu ya ja tsaki yana maida kallon sa kan Dr Amina din "Dr I think targade tayi sai kuma fever." "Garin Yaya amarya?" "Zamewa nayi Dr." "Bari na gani." Hannun ta nuna mata da kafar ta dan taba hannun kad'an tace mata sannu sannan ta fito da magungunan da ta taho dasu ta mikawa Tariq din "Dama Dr Sufyan ya fada min komai, so ga prescribe drugs din nan, sai kuma ko za'a dau jinin ta sai aje lab a yi mata Serum Pregnancy Test tunda yafi saurin nunawa." Dauke wuta jidda tayi kunya na lullubeta, shi kansa kunyar yaji amma ya dake yace "Bana jin Pregnancy issue ne." "No ai sai an gwada za'a gane Captain." "When last kika ga period dinki?" "Na'am?" "Feel free kinji? Yaushe?" "Three weeks ago." Tace tana hadiya yawu "Ok, yaushe kike expecting nashi kuma?" "Ending week d'in nan.". "Okh Masha Allah, bari mu jira ko zaki missing period din tunda naga mijinki baya so ya taba masa lafiyar jikinki" Dariya sukayi a tare, ya girgiza kansa "Dr ba haka bane ba, kawai dai..." "Shikenan ba damuwa ai, tasha wannan maganin ko ma da akwai pregnancy din ba zai effecting nasa ba, sai wannan da zata shafa Allah ya kara sauki." "Amin thank you so much." "Haba haba ba komai, Allah ya kara dankon soyayya." Sai ta mike *Bari na koma dan akwai patients sosai." "Ok, zamuyi magana da Dr Sufyan din akan duk charges din, thank you once again." "Ok, nagode sosai, amarya Allah ya kara sauki." "Amin nagode." Tace ta rakata da ido har ta fice shi kuma ya zauna yana mata kallon k'asa-k'asa "Amarya." Yayi mimicking voice dinta, murmushi tayi masa wanda yake sake narkar dashi, ji yake zai iya fasa tafiyar baki daya yayi zaman sa a nan kawai dan baya son yayi nisa da ita ko nan da chan. Mama ce ta kirashi a waya tace yazo tana son ganin sa, a dole ya fita ba dan yaso ba, ya barta tana bacci a daki ysa Amira ta dinga duba ta. Da la'asar ta tashi sai taji dan dama-dama, ta fito falon ta samesu suna kallo Salma tayi wanka ta sha uwar kwalliya kamar wadda zata gasar kyau, kuma ba laifi tayi kyau sosai sai dai illa daya kitson attachment din dake kanta da ta zubo dashi gadon bayan ta. Ran Jidda ne ya sosu har taji kishi sosai a ranta amma ta danne dan duk yadda Mama taso ta ga gazawarta zatayi kokari wajen toshe ta. Daki ta koma bayan ta dan zauna kad'an taje ta hada ruwa me zafi ta gasa kafar da hannun sannan tayi wanka ta fito ta shirya cikin hadadden lace din da akayi musu ita da Ya Safiyya da Umaima, sosai ya zauna das a jikin ta ya fito da ainahin kyawun jikin, bata shafa komai a fuskar ta ba sai eye liner da lipstick kadai da ta saka, sai turare da ta fesa sannan ta dawo falon a lokacin Amira ce kawai Salman ta shiga ciki, gud'a Amira tayi ta saki duk da bata iya ba,hakan ya jawo hankalin Salmar ta fito dan ganin abinda ake wa gudar sai taga ashe wai da jidda take, ranta ne ya baci tazo ta zauna a chunkushe "Na zata ma wani abun kike ma gud'a wallahi, kika saka na fito da sauri,Mtsw." "Kinsan fa ba zaki gane irin abubuwan nan ba, kin saka bakin hali a ranki da mugun nufi, shiyasa ba zaki taba banbance komai ba." "Amira?" Ta ware idon ta ranta na sake baci dan sosai Amiran ta soma kaita makura "Ni kike fada wa haka?" "Eh mana, menene abun tsaki dan Allah, jidda fa itace matar gidan nan, dole mu da muke gidan ta muyi respecting hakan, amma kamar ma baki san haka ba, haba!" "Ban sani ba, tunda ai ba ita ta gina gidan ba ko?" "Ba ita da gina ba amma dan ita aka gina, beside mace tafi iko akan gida fiye da mijin ta,dan babu me cewa gidan Ya Tariq sai gidan Jidda." "Kyale ta Amira, karki bata bakin ki dan Allah." A kufule Salma tace "Ina ruwanki? Bana son shishigi Malama." Murmushi Jidda tayi, "Kinsan nasan kece kika zubar da mai dazu ko? Sannan na zabi rufa miki asiri ko?" "Me yasa zaki rufa min asiri? Ai da kin fada." "Bana so ki tafi ne ban gama bakanta miki rai ba, baki gama ganin abinda zai saka zuciyar ki bugawa ba." "Thank you Jidda." Amira tace tana jingina mata da hannu, tsaki taja ta mike ta shige daki ta barsu suna mata dariya,a yadda take jin haushin Jidda zata iya yin komai, kuma ba in da zata har sai ta tarwatsa rayuwar Jiddan sai dai kowa ya rasa ayi biyu babu. *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (44) ***Dago ta yayi ya tallafo ta jikin sa yana tambayar ta me ya faru?" Hannun ta take nuna masa da yake mata zafi da zugi, hannun ya rike ta yi kara yayi saurin saki, ya dagata sama chak Amira ta matsa ya kai ta tsakiyar falon yana dudubabata. "Ina ne yake miki ciwo?" Yace yana kallon hannun nata da yaga tana son motsa yan yatsun, nuna masa hannun tayi tana hawaye, sai babban dan yatsan kafarta ta dama "Dukka hannun ne?" Ya tambaya yana maida hankalin sa kan kafar tata. Yan yatsun ta biyu ta nuna masa, ya gano tayi targade ne, tausayin ta yaji sosai, ya taimaka mata ta kwanta a cikin doguwar kujerar falon ya mike ya nufi daki don dauko wayar sa. Amira ce take mata sannu, tana kallon gefen rigarta da ya baci da mai "Mai ne ya zube akan hanyar?" Ta tambaya wani tunani na darsuwa a ranta "Um um, ni ban sani ba, ban zubar da mai ba ni, da na fito yanzu kuma babu komai, sai da na koma naji na taka mai." "Salma ta shiga kitchen din ko?" Tace ranta na baci "Eh." "Ita ta zubar da man kuma da gayya ta yi wallahi." "Wace ta zubar da mai?" Yace yana karasowa ciki rike da wayar sa a hannu yana son kiran Dr Sufyan, "Na'am?" Ta zaro ido tana mikewa daga durkuson da tayi a gaban Jiddan "Waye ya zubar?" "Mai ne inaga ya dan zube a kofar shine ban lura ba na taka." Jidda tace tana son dauke maganar "Ok." Yace yana share maganar kawai, yayi kiran wayar, be same shi ba, sai ya dawo ya zauna a gefen ta ya matso da ita kusa dashi yana kallon hannun yadda yan yatsun suka so ma kumbura haka ma na kafar "Sannu, suna ciwo?" Daga mishi kai tayi, ya dan taba kad'an tayi kara yayi saurin janye hannun sa "I'm sorry." Mikewa Amira tayi ta bar falon ta samu Salma ta gama shan tea din suna waya da Anty Nafi, a kanta Amira ta tsaya maimakon ta cigaba da wayar sai ta katse tana kallon ta "Lafiya?" "Me yasa kika zubar da mai a hanya kinsan Jidda ce zata shiga kitchen din." "Mai kuma? Yaushe?" "Oho, kinsan me nake nufi." "Ni ban zubar da komai ba, karki min sharri." "Nasan ke kika zuba a hanyar dan ta fadi, toh ta fadi kuma har tayi targade amma hakan be chanja yadda Ya Tariq yake son ta ba, sai ma kara musu closeness da yayi." "Sai kiyi kuma, ni ban zuba komi ba, kuma suyi ta kara son junan su ni ina ruwana?" "Da ruwan ki mana, tunda dai kin damu dasu, kuma wallahi gwara ma ki hakura Ya Tariq ba zai taba son ki ba, I'm sorry to say amma iyakar gaskiyar kenan, the earlier the better gwara kiyi ma kanki fada." "Zancen banza, ni ban san abinda kike fada ba, idan ma hakan ne laifi ne?" "Laifi ne mana, kina kokarin raba hadin da Allah ya riga ya hada." "Shikenan, haka din ne ma, kuma ki jira kiga yadda zan dawo da hankalin Ya T kai na." Dariya Amira ta kwashe da, ta zauna tana kallon Salmar kamar wata mara hankali ko tunani, ko giyar wake Ya Tariq yake sha ba zai taba son ta ba, ita kanta Maman tasani kuma bata masa sha'awar Salman kawai dai tana so tayi amfani da su ne wajen muzgunawa Jidda. "Sai ki bada himma, kafin me gidan ya gano kece kika zubar da man nan ya kada keyar ki, kinsan kuma ba zan rufa miki asiri ba wallahi." "Yanzu me ya hanaki fada masa?" "Jidda ce ta rufa miki asiri,da nasan ko sakan ba zaki kara ba, dama darajar Mama kikaci wallahi, baya so ya bata mata shiyasa." "Oh, ai da ta fada ita din ma, munafukar yarinya kawai." "Kissa tafi ki iyawa wallahi, tafi boka tafi Malam, ki zauna ki dauki course din yadda ake tafi da miji cikin ruwan sanyi, kinga idan kinyi aure kya samu na gwadawa." "Wai Amira ni da Jidda waye dan uwanki ne? Uwa daya fa uba daya iyayenmu ba wasa ba, amma kamar ma nice bare jidda ce yar uwarki." "Kusan hakan ne ai." Ta juyar da kanta cike da haushin Salmar ***A bacin rai Yaya ta nufi wajen Maman bayan ta samu labarin wai Amira da Salma na gidan Tariq har da kwana ma, bata san da wannan tsohon rashin mutuncin ba sai da Aunty ta fada mata, aikuwa ta wanke kafa taje ta samu Maman tana kirga lissafin wasu kudade a daki me aikin ta, ta shigo tace Yaya na mata magana a falo, ture abinda take tayi ta fito ta samu Yayan a tsaye ko zama batayi ba. "Barka da safiya Yaya." "Yawwa, yanzu Aisha tsakani da Allah abinda kikayi ya dace Kenan? Ki dauki yara yan mata kice su je su zauna da yaran nan, ina aka taba yin haka? Ko dan ita jidda ba yarki bace ba? Idan akayi wa daya daga cikin yaran nan zaki ji dadi? Itama fa mutum ce kamar kowa, iyayenta na son ta kamar yadda kike son naki yaran." "Baki kyauta ba, kuma kin bani mamaki, amma ba zan ce komai ba, ba kuma zance su dawo ba, amma fa ki sani, shi sharri dan aike ne, dan haka ki kula, ki kula!" Sai ta juya tayi ficewar ta, dan tasan Maman ba zata tanka ba, dama kuma ba dan ta tanka tazo ta same ta ba, amma ta fada mata, kuma idan har ita din ba mahaukaciya bace zatayi abinda ya dace, mutane suna da masifar son kansu, shiyasa sam bama cigaba, dan ka shine d'a, d'an wani kuwa babu ruwan ka da duk ma halin da zai shiga. Shiru Maman tayi bayan fitar Yayan, a kasan zuciyar ta, tana jin bata kyauta ba, amma kuma tsanar Jidda ya danne rashin kyautawar, shiyasa har take jin batayi komai ba, ita dai abu daya kawai take so, Jidda ta kyale mata danta, bata bukatar sake hada wata alaka da Halima bayan wadda ta hada a baya. Tana zaune ya zubo mata pepper soup din da aunty ta kawo musu da chips, ya zauna ya saka fork ya debo chips din bayan ya hado da tsokar naman ya nufi bakin ta,a kunyace ta bud'e ya shiga bata yana hada mata da tea me zafi, sai da taci ta koshi sannan ya ajiye ya sa tissue yana goge mata gefen bakin ta yana kallon bakin, yana son dan mitsitsin bakin ta har baya iya dauke ido daga kansa, yana son kissing dinsu a ko da yaushe saboda softness dinsu, daurewa yayi ya share ya zubo kad'an yaci dan already ya karasa golden morn din da ya fara sha. Sake kiran Sufyan yayi still no answer sai yayi tunanin ko yana da emergency case. Ya kyale shi idan yaga kiran zai biyo yasan. Har azahar tayi be kirashi ba, ga hannun ya kara tsami sosai sai ya yanke shawarar kiran Aunty ya kira ya fada mata in brief duk da be fada mata yan yatsu biyu ne da na kafa ba, cewa tayi zata turo jummai daya daga cikin masu aikin gidan da ke bq ta iya gyaran targade, dan kwanaki Usman yayi ita kuma ta gyara masa. Godiya yayi ya ajiye wayar. Baa dade ba sai gata Sam ya kawo ta, ya bud'e mata kofar da kansa ta shigo ta gaishe shi ya amsa yace ta shiga, ta samu Jiddan a zaune suka gaisa ta kalli hannun da kafar, sannan ta kalli Tariq din "A kawo wuka da manja." "Wuka?" Yace "Eh yallabai, sannan dole sai an rike ta, targade daya ma ya aka kare bare har uku, Allah dai ya kiyaye gaba." "Me za'a yi da wukar? Yanke hannun zaa yi?" Jidda tace hawaye na zubo mata dan ta taba yin targade tasan azabar sa "Ba abinda za'a yi da ita, kawai zan dan yi amfani da ita ne." "Amira!!!" Ya bud'e muryar sa ya kirata, ta fito da sauri yace ta kawo knife da manja, taje ta kawo ta zo ta zauna tana kallon ikon Allah, matar ta shafa manjan a jikin wukar sannan tace Tariq ya rike Jiddan, ya matso ya zauna yana jawota jikin sa ya shiga tapping bayan ta "Calm down,ba zai ciwo ba, I'm here." Kankame shi tayi tana chusa kanta cikin jikinsa, matar ta kama hannun ta dora wukar a jiki ta dan yi yan sakonni sannan ta cire ta fara taba hannun, ai jidda bata san sanda ta hau kuka wiwi tana kokarin kwace kanta, ya matse ta tausayin ta na kara kamashi, kuka take sosai tana kiran Baffan ta har akayi biyu sannan yace a barta ta huta, ya tashi da sauri ya karo AC din falon saboda yadda take zufa, ya rungume ta yana mata sannu, juyar da kai matar tayi sai kuma ta mike tace zata dan fita waje, tana fita Amira ma ta tashi, sai a lokacin taga Salma a jikin kofar da zata kaita dakin da suke, yi tayi kamar bata ganta ba ta wuce ta. Kanta yake shafawa yana jera mata sannu, har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take saukewa, har jikin ta ya fara zafi saboda azaba, ba dan ciwo bane da cewa zai a kyale ta haka amma dole ayi na kafar dan yasan ba zata iya taka kafar na idan ya kwana. "Ta zo ta karasa miki ko?" Da sauri ta hau girgiza kai "Dan Allah a barshi, zai warke da kansa, Dan Allah zan mutu wallahi." "Shshhh, ba zaki mutu na, kuma ba zai zafi kamar wadanchan ba, kiyi hakuri a karasa kinji? Pleaseeee." Da ka ta amsa masa da toh, ya leka ya kirawo matar ta dawo, ta kama kafar itama ta gyara aikuwa tasha kuka sosai, ana gamawa ya dauke ta chak ya wuce dakin sa, ya kaita ya kwantar a saman gadon ya zame mata hannun rigar ta zuwa kafadarta yana jera mata sannu. *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (46) Assalamualaikum NAFISAT K ABDULLAHI Is an actress in the kannywood industry She's a singer and can sing all types of songs You can't afford to miss her newly released song named *KADDARATA* part 1-4 on her YouTube channel *OFFICIAL FEENAT* You can only click on this link and stand a chance to listen and watch her amazing video https://youtu.be/t__84EwU7Fo Dont only enjoy the emotional video but also *SUBSCRIBE* to anable you to be notified when ever she upload another video Like and drop your comment under the video to encourage her do more of that . The only way you can support and encourage her is by *SUBSCRIBING* to her YouTube channel below https://youtu.be/t__84EwU7Fo She is used to noticing those following and commenting on her videos . *GUESS WHAT*? https://youtu.be/t__84EwU7Fo Click and see for yourself Thank you so much ***Maganar tafiyar Mama tayi masa dan tana so taje kano a weekends din da za'a shiga idan akwai abinda zata taho masa dashi, ko da tayi masa maganar tafiyar sai yace yayi postponding dinta har ya tura musu mail ma duk da basuyi reply ba "Amma me yasa zaka daga? Ba kace suna jiran ka ba?" Ta tambaya cike da mamakin sa "Wani abu ne ya taso Mama, dole na fara solving din matsalar kafin na tafi." "Matsalar mecece?" "Umm... Ba wani babban abu bane in sha Allah, karki damu." "Dole dai akwai dalili, haka kawai ba zaka daga tafiya ba." "Allah yasa haka ne mafi alkhairi " "Amin." Tace a gajarce "Yaushe Baba zai dawo? Ban sameshi a waya ba tunda ya tafi " "Mun yi magana jiya amma be maganar dawowar ba tukunna, kasan baya fada yanzu sai ana i gobe." "Fasa tafiya sukayi da Auntyn?" "Oho ban sani ba." Murmushi yayi kawai ya cigaba da zama shiru, itama tayi masa shiru sai da Maryam ta fito ta gaishe shi sannan ya tuna da maganar su Amira "Mah tunda ba tafiya zan ba sai su dawo ko?" "Akan ka suke zaune? Ko ita shafaffiya da mai din ce tace su tafi?" Shiru yayi mata dan be san me zai ce mata ba, ba kuma yaso tana involving Jidda a ciki dan da yasan yadda zata dauki maganar da be yi ba. Jin yayi shiru yasa itama tayi shiru suka cigaba da zama a haka, sai chan ya tashi yace zai tafi lokacin ana shirye-shiryen kiran sallar magriba, sallama sukayi ya wuce masjid yayi sallah suka gaisa da wasu mutanen Baba da suke yawan zuwa gidan sannan ya wuce gida ba tare da ya koma ciki ba. Yana daf da shiga gidan shi da Faisal Safiyya ta kirashi, suka gaisa tayi masa maganar Salma da dalilin zuwa gidan nasu, shiru yayi yana jin ta har ta gama bayanin da ya riga ya sani shiru kawai yayi dan baya son batawa Mama, sai dai maganar zubar da man da tayi da niyya ya matukar bashi tsoro dan zata iya aikata komai, dama yayi tunanin itace tunda dazu da yaji suna maganar da Jidda da amira akan man da aka zubar din amma sai Jiddan ta rufe maganar, ransa ne yaji ya baci, yace wa safiyyan karta damu yayi assuring dinta babu abinda zai faru sannan sukayi sallama ya kashe wayar yana tunanin yadda zai bullowa al'amarin Maman dan yarinyar ta kai shi karshe musamman da ya tuna bakar wahalar da Jiddan tasha dazun. Dama ya ga take taken ta sharewa yayi kawai yana jiran right time dan duk wani action da zai dauka akan Jidda abin zai kare, shiyasa ya kyale tun farko amma yanzu yasan abinda zai kawai ya kawo karshen wannan drama din, jiran Baba kawai yake ya dawo suyi magana idan har ya bashi goo ahead shikenan. Shigar Jidda daki kenan ya shigo gidan, tana toilet bata ji shigowar sa ba, wuf Salma ta fito falon ta tsaya tana jiran shigowar sa, ta chanja kayan jikinta zuwa kanana bodyhug da jeans da ya kamata sosai, kanta babu ko dankwali sai attach din da ta bazo har gadon bayan ta. Turo kofar yayi cike da karsashin ganin ta, dan ji yake kamar yayi shekara be sa ta a idon sa ba, so yake yaga jikin nata duk da sau biyu yana kiran wayarta bata dauka ba sai yayi tunanin ko baccin take har lokacin sai kawai ya kyale ta. Annurin fuskar sa ne ya ringa janyewa yana maye gurbi da bacin rai, tsananin bacin ran ganin shigar iskancin da yarinyar tayi ta kuma toge a hanya tana masa kallo tamkar tsohuwar mayya. "Ya T Welcome." "Amira!!!" Ya kwala mata kira, a guje ta fito itama Jidda ta fito da sauri, "Jeki fito da kayan da kuka zo dasu." Yace zuciyar sa na tafasa, da sauri ta juya jidda da ta tsaya daga hanya ta kasa karasowa ya kuma ki yarda ya kalli sashen da take ta sake jingina da bangon wajen tana kallon ikon Allah. Amira ce ta fito ya nuna mata hanya "Ja wannan mahaukaciyar yarinyar ku fice min daga gida." "Ya Tariq nice mahaukaciya?" "Shut up stupid, Allah Amira kika bari na kara magana sai na baku mamaki, kije ki samu faisal ya sauke ku a gida." "Ke kuma,wallahi wallahi ko kafar ki na gani a hanyar gidan nan sai na tattaka ki na zubar, stupid girl." "Muje malama." Amira tace tana hararar ta, tsayawa tayi taki motsawa jin tarin Jidda a bayan ta, ba'a taba humiliating dinta irin yau ba, kamar an dasa ta a wajn haka ta kasa motsawa, sai da Amira ta fizgi hannun ta sannan ta iya daga kafarta guda daya sannan ta motsa dayar. Wuce su yayi yana kokarin daidaita fushin da yake ciki, ya nufe ta ganin duk ta tsorata da yanayin sa. Ji tayi kawai yayi hugging dinta da sauri yana sauke ajiyar zuciya, kafin ya ja hannun ta su bar falon ba tare da ya sake bi ta kan su Amira ba. Tun a mota Salman ta dinga rusa kuma Amira bata tanka mata ba, dama tun ranar farko taso ya Tariq din ya kore su amma ya kyale su, ita tana ta danna waya bata ma lura da falo Salman ta fito ba, ta dauka ma tana toilet ashe yar iskar yarinya wai tarar Ya Tariq din tazo,lallai bata san waye shi ba, su kansu da suke ciki daya basa zama tare dashi haka ba mayafi bare har suyi wata banzar shiga sam basu taso da wannan rayuwar ba, akwai limit a komai idan aka cire ma Ya Fauwaz da Ya Safiyya babu Wanda a cikin su Ya Tariq din yake wata doguwar magaana dasu bare har su samu fuskar raina shi, ita Amira da yake ma itace karama kuma akwai tazara sosai a tsakanij su tsoron sa ma take ji shiyasa bata so zuwan su gidan ba, shima kuma yasan ba zata so ba amma ya zatayi da Mama? Tun farko basu iya cewa Maman a ah ba a komai tace tunda dama ba tarbiyya bace, shiyasa har Ya Tariq din baya ketare maganar ta sai dai a irin case din yanzu na jiddah da kuma ko waye tasan hakan zai yi tunda dai tsanar da tayi ma Jiddan ba ta da wani kwakkwaran dalili. motar na gama parking Amira ta fice ta wuce part din Yaya dan ma kar su Mama su cikata da tambaya dan yau tasan akwai rikici a wajen Aunty Nafi akan shalelen ta, dan bata sani ba ma ko kafin fitowar ta daga daki Ya Tariq din ya dan mammari fuskar ta. Tunda suka shiga dakin ya zauna be ce uffan ba, tana ta satar kallon sa yayi nisa a tunani, he looked disturbed kamar akwai wani abu bayan abinda ya faru yanzu da ya dame shi. Ji tayi duk ta damu da damuwar sa dan tunda tazo gidan bata taba ganin damuwa karara kamar haka a fuskar shi ba. Kasa sukuni tayi, ta taso tazo gabansa ta zauna ya kalli babban dan yatsan kafar tata sannan ya kalli fuskar ta, sai ya zamo ya zauna a kasan kan carpet din da ke gaban gadon ya kama hannun nata "Sun daina ciwon?" Yace bayan ya hadiye yawun da ya taru a makoshin sa, gid'a masa kai tayi, ya lura tana son yin amfani da kanta wajen amsa tambayar da amsar ta dari bisa dari. "Kafar fa?" "Da sauki." "Basu daina ba ko? Raguwa ciwon kawa yayi." "Eh." "Owk sannu." "Uhumm." "Shine baki fada min Salma ce ta zubar da man da kika zame ba ko? Yanzu idan da tsautsayi kika karye fa? Ko wani abu worst than this ya faru? Shikenan sai kiyi shiru?" "Bana son ranka ya baci ne, shiyasa kawai na kyale, tunda Allah ya kiyaye ma." "Karki kara irin wannan, babu amfanin zaman mu da ita in dai cutarwa zata shigo ciki." "In sha Allah ba zan kara ba." "Good." "Shikenan?" Tace ganin be saki ran nasa ba har lokacin, girgiza mata kai yayi yadda take yi yace "Ba shikenan ba." "Ok." Tace a sanyaye. "Ciwon ya daina?" Ya sake tambayar ta bayan be dade ta tambayar ta ba "Kad'an yake yi." "Ok ." Sai ya mike tsaye ya hau rage kayan jikin sa yana jin yadda zuciyar sa ke neman yi masa ingiza me kantu. Tashi tayi ta fice ganin yana neman cire kusan dukka kayan jikin nasa a gaban ta, tasan kila ya manta tana nan shiyasa . Chanjawa yayi ya fito falon ya zauna bayan ya jona system dinsa ya bud'e ta ya fara aiki akanta Wajen goma na dare suna zaune shi yana ta aiki a system din ita kuma tana kwance a gefen sa tana kallon film bacci na fizgarta, wayar sa dake ta side din ta tayi kara, hannu ya miko mata still idon sa na kan system din ta mika masa ya daga ba tare da ya kalli number din ba, ya kuma sata a handsfree "Hello Captain." Muryar mace ta ratso cikin wayar ta dire a kunnen Jidda da gaban ta yayi wani irin faduwa "Wa ke magana?" Yace yana maida hankalin sa akan wayar "Yasmin ce." "Yasmin?" "Don't tell me baka gane, ohh my God yanzu Tariq ka manta Yasmin?" "Sorry, ya akayi?" "Lord! Kana nan dai yadda na sanka, ba abinda ya chanja daga classy Tariq din da na sani who's always ignoring me " "How are you? Ya komai?" "Fine sha, sai dai missing dinka ka tafi ba sallama, yanzu ka kyauta kenan?" Kallon gefen Jidda yayi yaga ta tashi zaune, tana gyara dankwalin kanta da ya sabule mata, sai kuma ta mike ta shige ciki yana kallon ta. "Sorry Yasmin, nagode sai anjima." "Wait..." Kit ya katse ya mike yana rufe system din yabi bayan ta Tana zaune hawaye na tsere a kan kuncinta, kishi da haushin wadda aka kira da Yasmin ya cika mata zuciya har take jin kamar numfashin ta nayin sama-sama, da gaske take kishin sa musamman akan wannan unknown Yasmin din da take jin kamar tayi daidai ta dace da spec din Ya Tariq din. Turo kofar yayi ya shigo tayi saurin sa bayan hannun ta, ta share fuskar ta, amma duk da haka ya ganta. "Jidda, are you ok? Menene? Why are you crying?" "Ba komai." "Fada min, ciwon ne?" Girgiza masa kai tayi tana jan kukan da ke taso mata "Come here." Ya jawota jikin sa sai kawai ta fashe da kuka, kukan da ya saka shi gaba daya yaji yayi loosing control dinsa, dama tun dazu yana ta kokarin hana zuciya da gangar jikinsa, amma sai gashi jidda na neman ballo ruwa, rarrashin ta ya ke yi amma sam taki yin shiru, dago ta yayi daga danna fuskar ta da tayi a kirjin ta, ya hade bakin su waje daya ya shiga kissing dinta da sauri da sauri. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (47) Malama's Citadel 08035625833 Zaria kaduna state Original Ayu oil Infection and Cleansing set na maza da mata Tsumi Tightener Matsi me kyau Kaza Tsarki herbs ***Saurin hadiye kukan da take tayi ganin gaba daya Ya Tariq din ya chanja mata zuwa wani daban, yana yi mata wasu abubuwan da kwakwalwarta ya gaza dauka, gigicewa tayi ta hau kokarin tashi take ya hanata yana girgiza mata kai "Please Jidda, dan Allah." "Dan Allah kayi hakuri." Jikinta ya hau rawa kaamar mazari, ba zai iya ba, ba zai iya hana kansa ba, amma yayi alkawari zama cool, ba zai cutar da ita ba,gyara mata zama yayi a jikin sa yana shafa mata kanta, "Shsss, kiyi shiru kinji?, ba zai ciwo ba, I promise ba zai ciwo ba." "Dan Allah kayi hakuri " Ta cigaba da kuka tana cigaba da son tashi, sake matse ta yayi yana cigaba da bata hakuri, har ya samu ta nutsu, tallafo fuskar ta, yayi yana kallon cikin idon ta. Motsa bakin sa yayi a hankali yace "Ina sonki Jidda!" "I love you so much, har bansan yawan son da nake miki ba, bansan yaushe ba, kawai na samu kaina in love with you, you possess all the qualities da nake son mace, i was foolish at first da na fadi abubuwan nan, and it's just my hallucination, ke nake so, only you, and you alone." Ajiyar zuciya ta sauke tana boye fuskarta a tsakanin kirjin sa. Kansa ya daga sama yayi murmushi yana ciro ta daga chest din nasa yace "Allow me to show you how much I love you,I promise to be a gentle man." "Tsoro nake ji." Tace idon ta na ciccikowa "Comman karki kuka, ba wani abu bane ba, pleaseeee." "Kin amince?" Yace yana murza mata tafin hannun ta a hankali, da ka ta amsa masa duk da zuciyar ta kamar zata bud'e ta fito saboda tsabar tsoron da take ji. Murmushi ya sakar mata yana lumshe idon sa "Thank you Jidda!" Yace yana gyara mata kwanciyar, kulle idon ta tayi gaba daya kukan na cigaba taso mata, tana jin kamar tace bata amince ba, kaamar tace ta fasa ya kyale ta, sai dai kash! Babu irin duka da yakushin da batayi masa ba, ta dinga kiran Baffa, Aunty har Amira sai da ta kira tana neman agaji amma ko a jikin sa, be masan tana yi ba, sai jaddada mata irin son da yake mata yake da bata gane ko mai sai bakar azabar datake ji har cikin kwakwalwar. Duk da da gaske a hankali ya tafi da ita amma still ta sha bakar wahalar ,irin wadda bata taba tunani ko hasashe ba, bata san haka abun yake ba, bata kuma san yadda zata misalta ba. Kukan ta cigaba da yi amma k'asa-k'asa, sai jan ajiyar u yayi wajen ta tayi saurin matsawa tana rokon sa cikin muryar ta da ta dashe sosai saboda tsabar kuka. "Dan Allah kayi hakuri wallahi ba zan iya ba." "Ba abinda zan miki I promise, I'm sorry." Rungume ta yayi ta cigaba da kukan yana jin ta, hannun sa na saman kanta yana shafawa a hankali, be san da wanne baki zai amfani wajen bata hakuri ba,sai kawai yayi shiru ya cigaba da shafa kan nata har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take jerawa, rungume ta yayi kam-kam yana jin kamar ya bude zuciyar sa ya saka ta a ciki. A hankali bacci ya soma daukar ta, sai kuma zazzabin da ya dawo ya sake rufe ta, gyara mata kwanciyar yayi ya zare jikin sa a hankali ya mike ya nufi toilet yana jin kansa yayi masa nauyi sosai, ya dan jima a ciki ya fito yana goge jikin sa da towel, ya shinfida abun sallah bayan ya zura doguwar jallabiya ya dan karo fan din sannan ya tada sallah. Rara'a biyu yayi ya zauna yayi addu'a sosai sannan ya godiya Allah bisa niimar da yayi masa duk da ya saka san ransa bayan zabin Allah shine babba zabi mafi dacewa. Motsi yaga tana yi ya mike da sauri ya isa wajen ta, yana kallon yadda take ya mutse fuska alamun rashin jin dadi, tausayin ta yake ji gaba daya da dana sanin abinda ya aikata mata, yaso ace ba yanzu ba, yaso ace sai sun kara shakuwa sosai, amma kuma babu yadda zai. Rike ta yayi ta daina motsin ta cigaba da baccin a wahalce, jikin ta zafi sosai kamar wuta, so yake ya taimaka mata ya rage mata zafin jikin amma baya so ta tashi a gigice dan duk ta riga ta tsorata dashi. Magungunan ta yaje ya dauko yazo ya ajiye a bedside ya hau gadon a hankali yadda ba zata tashi ba, ya kwanta a bayan ta ba tare da ya hada jikin sa da nata ba, ya leko fuskar ta ya gyara mata gashin ta da ya hargitse ya bazo har saman fuskarta. Wajen asubah ta farka ta ware idon ta akan shi sai abinda ya faru ya dawo mata, da sauri ta sake matsawa daga kusa dashi, ta sakko a hankali daga gadon tana ya mutse fuska ta shiga toilet, karar bud'e kofar toilet din ce ta tashe shi, ya kalli bangaren datake kwance ganin bata nan yasa ya tashi da sauri ya bi bayanta ya bud'e toilet din da turo shi kawai tayi bata rufe ba. Tana tsaye tana hawaye ya shigo, ya riko ta yana kiran sunn ta "Jidda?" "Menene? Akwai abinda yake miki ciwo ne?" Daga kanta tayi tana jan kukan, "I'm sorry dan Allah kiyi hakuri." "Ni ka fita." Tace tana cigaba da kukan, "Taimaka miki zan, zaki ji sauki." "Um um ni bana so." "Kiyi hakuri dan Allah, ki bari na taimaka miki kinji?" Noke kafardar ta tayi, "Shikenan, shikenan zan fita, I'm sorry." Sai ya juya ya fita ya ja mata kofar, ya cire bedsheet din ya saka a gefe ya dauko wani a closet ya saka sannan ya dawo ya tsaya a jikin kofar yana jiran ta fito, ta dade sosai har ya fara tunanin komawa ciki amma sai gata ta fito tana jan kafar ta, yayi saurin tarar ta, ya kai ta ta zauna a gefen gadon ya dauko towel ya hau goge mata kanta. "Sanyi." Tace tana kankame jikin ta, saurin kashe komai yayi ya bud'e kayan sa,ya dauko mata jallabiyar sa, ya saka mata sannan ya taimaka mata ta kwanta, kumburarrun idon ta ya kalla ya girgiza kai lokacin aka soma kiran sallar asubah, alwala yaje yayi yazo yace ta tashi suyi sallah, ta mike tana kin kallon sa ya bata Hijab ta saka har lokacin sanyi take ji sosai sukayi sallar sannan ta koma ta kwanta ya lullube ta ya fito zuwa kitchen ya hado mata tea me kauri ya dawo dakin ya tashe ta zaune tasha sannan ya bata magungunan ta,tasha suma sannan ta koma ta sake kwanciya, bata dade ba baccin ya sake dauke ta. A gaban gadon saitin fuskar ta ya durkusar da guiwowin sa yana kallon kyakkyawar fuskar ta da tayi ja saboda tsabar kuka, saman dogon hancin ta ya kai hannu wajn wani ja ya taba kad'an yana girgiza kansa, a yadda take fitar da numfashin ya tabbata taji jiki sosai, dama kuma ga ciwon targaden da ya dinga kokarin hana kanshi akan hakan amma be san me ya hau kansa ba, ya kasa hakura bayan yasan tana bukatar tayi healing yazo ya kara mata wani ciwon akan wanda take fama, be kyauta ba sam, kuma zata iya yi masa wani irin kallo. Hannun sa ya kai ya shafi gefen fuskar ta. "I love you Little Jiddah." Sai yayi kissing dinta a saman goshin ta, sannan ya mike ya fita daga dakin ganin rana ta fito sosai. ***Wayarsa dake yashe akan kujera tun sanda Yasmin ta kirashi ya ajiye be saka bi ta kanta ba ya dauka ya ga missed calls da yawa, da sauri ya cire lock din ya shiga call log ya tarar da 15missed calls daga Yasmin sai 5 daga Mama sai Fauwaz guda biyu. Duk da dama yasan Mama zata kirashi amma be yi tunanin har missed calls haka ba, kiran ya bi yana kishingid'a a saman kujerar yasa hannun sa yana shafa saman kansa dake masa ciwo sama-sama. Bata dauka ba har ta katse ya sake kira nan ma no answer sai kawai ya ajiye wayar yana tunanin yadda zasu kwashe da maman yana kuma fatan ta fahimce shi ko yaya ne. Wani tunani ne yazo masa sai ya sake daukar wayar ya kira Fauwaz bugu daya ya daga. "Ya Tariq ina ka shiga?" "Fauwaz, bacci nayi na bar wayar a falo naga miss calls din Mama da yawa, hope lafiya?" "Ba kalou ba wallahi, akwai babbar matsala." "Toh! Me ya faru?" "It's a complicated case wallahi, ni dai da zaka zo gidan yanzu kawai." "Jidda bata jin dadi ba zan iya barin ta ba, she needs me." "Ayya, Allah ya bata lafiya, kaga Maman ma gasu nn sun fito ita da Aunty Nafi da Salma, bari naji zan kiraka." "Ok, kace wa Maman na kirata bata daga ba." "Okh ." Yayi hanging yana nufar wajen su, "Mama,fita zakuyi?" Wani kallo tayi masa ya sunkuyar da kansa k'asa dan yasan halin da Maman take ciki ba karami bane ba "Tariq be kiraka ba?" "Ya kira, ya kira ki ma baki daga ba." "Good, idan ma yayi hakan ne dan kar mu hadu ni yanzu zanje har gidan nasa na same shi." "Gida kuma Mama? Why not ki bari yazo, za'a iya solving issue din nan ba sai kinje ba." Kallon shashen da Aunty Nafi da Salma ke tsaye tayi ranta ya kara baci idan ta tuno da abinda Salmar tace wanda tasan sharri ne kawai tayi wa Tariq din kuma da tainakon Nafin da tasan haka zasu yi mata da tun farko bata yarda da shawarar Nafin ba. "Ina Sam?" Tace tana share maganar Fauwaz din, da sauri ya karaso ya duka ya gaishe ta, "Muje." "Mama bari na kaiku." "Zaka iya biyo bayan mu, ku shiga muje." Tace wa aunty Nafi ta shiga ita,zagaya wa sukayi Salma ta shige chan baya, security daya ya zauna a gaba sai Mama da Aunty N a tsakiya. Da sauri Fauwaz ya nufi wajen motar sa ya shiga yana kiran Ya Tariq din a waya amma sam taki shiga, key yayi ma motar ya bi bayan su yana cigaba da gwadawa. Yana kwance a falo lokaci zuwa lokaci yana lekawa ya dubo Jiddan amma sai yaga tana bacci, sai ya dawo. Har bacci ya soma daukar sa yaji ana knocking a chan kofar main entrance din, Godiya ce ta fito daga kitchen taje ta bud'e sai ya mike ya fito daidai lokacin da Mama, Aunty Nafi, Salma sai Fauwaz dake bayan su suka shigo, da kallo ya bisu irin kallon mamakin nan, kafin ya karaso yana nazarin fuskar Maman da take a hade tamkar an mata mutuwa. "Mama? Welcome." "Ina ka ajiye wayar ka nake da kiran ka?" "A falo na barta." "Good, zauna." Tace tana nuna masa wajen zama ya zauna a darare duk jikinsa yayi sanyi dan be san dalilin zuwan nasu ba "Salma, maimaita abinda kika fada mana ni da mamanki." "Na'am?" Tace tana kallon TARIQ din da itama shi yake kallo "Kiyi magana mana ba kallon sa zaki tsaya yi ba." Aunty Nafi tace tana tamke fuska "Dama, dama ya Tariq ne." Saukar da kai Mama tayi wani irin abu na taso mata tun kafin Salman ta yi maganar da ta gigita ta, ta kuma hanata bacci a daren jiya ko runtsawa bata yi ba. "Muna jinki." "Dama shine ya ke taba ni yana min wani abu shine jiya da ya dawo ya fara min wata irin magana ni kuma nace bana so sai ga jiddah nan ta fito shine ya kore mu yace mu bar masa gida." Wajen sakwanni biyar maganganun nata suka dauka kafin su kai sakon zuwa kwakwalwar Tariq wanda ya kura mata ido kawai ya kasa furta ko kalma daya. "Kaji abinda tace?" Mama tace cike da kunya da takaicin hali irin na Nafi "Ya Tariq kana ji kuwa?" Fauwaz yace ganin kamar be san me ake cewa ba. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (48) A hankali yanayin fuskar sa ya shiga chanjawa zuwa tsananin bacin rai, cikin kankanin lokaci kamannin sa suka sauya ya koma tamkar wanda be taba dariya ko murmushi ba a rayuwar sa, kallon yarinyar yake yana jin zai iya kakkaryata ya zubar a wajen idan har ya biyewa zuciyar sa. "Baka ce komai ba." Mama tace tana kallon sa "Me zai ce? Bashi da abin cewa ai, ni wallahi an cuce ni wallahi an cuci rayuwa ta." Anty Nafi tace tana fashewa da kukan munafurci, be ko kalli in da take ba, ya cigaba da kallon Salman ita kuma ta sunkuyar da kanta kasa dan kallon nasa ya fara bata tsoro, ba ita ba har Anty Nafin tsoro ya shige ta ganin yadda kirjin sa yake dagawa. "Tariq!!!" Mama ta kwala kiran sa, ya juyo a nutse yana kallon ta tar, "Na'am Mama." "Baka ji me Salma tace ba?" "Naji Mama." Yace yana kokarin daidaita calmness dinsa "Amma ba zaka ce komai ba?" "Bani da abinda zan ce Mama, in dai har wannan dakikiyar kazamar kuchakar yarinyar nan zata zauna ta tsara wannan maganar kuma ku zo dan tabbatarwa, bani da abinda zance akai." "Tariq karka yi kokarin chanja maganar nan, kasan dai Salma ba zata maka karya ba ko?" Anty Nafi ta fada ganin kamar yanayin da yake ciki ya sassauta "Da mahaifiyata nake magana ban sa dake ba!" Yace mata a fusace, da karfi. Tsit tayi bata kuma cewa komai ba, ya maida hankalin sa kan Mama ya cigaba da magana "Idan har yarinyar nan ta kara minti daya a gidan nan wallahi wallahi sai na ajiye alaka da komai na kakkaryata na zubar a wajen nan,." "Saboda baka son gaskiya ko? Wallahi ba zan yarda dake ni sannan a hanani kuka ba, wallahi mahaifin ka zan gyayawa, ko ka auri Salma wallahi ko na fada masa, kunsan dai dan siyasa ne baya so sunan sa ya baci ko?" "To hell with you!" Ya dake mata tsawa "Ki fadawa duk wanda zaki fadawa wallahi, I don't care!" "Fauwaz, take them out." "Calm down Ya Tariq." "Su fita nace!" "Tashi Nafi, ma karasa maganar a gida." Mama tace tana kallon yadda yake huci "Dole ya auri Salma wallahi dan ba zai lallata min rayuwar yarinya kuma yazo yace ba zai aure ta ba." "Muje." Tashi tayi tana cigaba da kumfar baki, Jidda da tun dazu take jin muryar sa a sama ce ta lallabo ta fito sanye da rigar sa sai yar hular da ta rufe gashin kanta,sun tashi kenan ta fito kallo ya dawo kanta, da sauri ta juya zata koma a tunanin ta basu ganta ba, sai jin Fauwaz tayi ya kira sunan ta "Aunty jidda." Tsayawa tayi ta juyo cikin matsananciyar kunya ta karaso falon ta duk'a kad'an tace "Ina kwana?" A gajarce Maman ta amsa tana kauda kanta dan kallo daya tayi wa Jiddan ta gano wani abu, Anty Nafi ta gaisar amma bata amsa ba sai Salma da ta banka mata harara, suka fice daga falon ya rage saura Tariq din da Fauwaz, zama Tariq din yayi yana tallafe kansa da hannayen sa biyu. "Ya Fauwaz ina kwana?" "Lafiya lou Jidda, pls ki kula da Ya Tariq bari na dawo." Sai ya juya shima ya fice daga falon ya same su har sun shiga mota. A gaban sa tayi kamar kneel down tana kallon hannun sa da ya tallafe fuskar sa dashi, hannu tasa ta kama hannun nasa ya dago idanun sa da suka rini sukayi jajawur ya zuba mata tsoro ya kamata ganin yadda suka koma. "Ya kike jin jikinki?" Ya fada muryar sa a dashe kamar wanda yasha wani abu "Naji sauki." "Ok." "Baka da lafiya ne?" "I'm furious Jiddaaaa." Sai ya saka hannu ya jawo ta jikin sa, ya rungume ta ko zai samu saukin abinda yake ji. Fauwaz ne ya dawo ciki sannan ya cikata yana gyara mata jikin rigar "Jeki ciki kinji? Karki damu." Jiki a sanyaye ta shige ciki ya kalli Fauwaz yana tashi tsaye "Ya za'a yi Ya Tariq? Menene abun yi? Kasan irin wannan sharrin issue ne very complicated, sannan kamar bata sunan mutum ne, hatta Baba idan abun nan ya fita sai sunan sa ya baci sosai duk da ba gaskiya bane." "Fauwaz I don't care duk abinda duniya zata ce wallahi, this is a great lesson da ya kamata Mama ta dauka, da tun farko ba'a turo yarinyar nan gidan nan ba, ya hakan zata faru? But sai ta biyewa Anty Nafi which ita da kanta tasan how evil that woman is, duk saboda kishi, kishin da bashi da maaana bare tushe." "But Aunty Nafi zata iya aikata komai to tarnish your reputation in dai har bukatar ta zata biya." "Har abadah wallahi, kuma in dai ta cigaba da pushing akan maganar nan wallahi sai na bata mamaki ita da ballagazar yar ta." "Calm down dan Allah, don't frustrate your self mu zauna a samu solution." "Ba wani solution Fauwaz, tunda hakan suke so hakan za'a yi, muga wanda zai fasa ni dasu." "Amma idan suka samu Baba da maganar fa? Kana ganin zai yarda?" "I can't say ko zai yarda ko bazai yarda ba wallahi, ni dai tunda nasan ban aikata ba shikenan." Yayi maganar yana yarfa hannun sa gefe daya cikin bacin rai "Nasan kana cikin bacin rai." "Very! Kasan yadda sharri yake kuwa? Sharri irin wannan? ba zaka gane ba." "I totally understand, nasan yadda kake ji, it's not easy amma kayi hakuri dan Allah, mu bi komai a sannu wasu matan are cunning yadda baka taba tunani, shaidan haka suke wallahi." "Allah ya kyauta." "Amin ya Allah, inaga bari naje duk yadda ake ciki zan fada maka." "Ok thank you." Ya mika masa hannu sukayi musabiha sannan ya tafi shi kuma ya cigaba da zama a wajen ya kasa mikewa bare ya shiga ciki. ***Tunanin abinda ya kawo Maaman take tunda ta koma duk da taga Salma ta kuma san kila akan abinda ya faru jiya ne amma kuma ai be ci ace har sai Maman sunzo da kanta ba, bacin ran dake fuskar Ya Tariq din yasa ta tabbatar akwai matsala babba, wanda ta alakanta da yadda Maman bata son auren su. Shiru shiru be shigo ba gashi bata son komawa ko basu gama maganar ba, zama tayi ta cigaba da jiran sa har ta gaji ta shiga wanka tana fitowa ta ganshi yana duba wasu takardu, dagowa yayi ya kalle ta kad'an ya cigaba da abinda yake yi, wucewa tayi ta dauki kaya a closet ta saka daidai lokacin ya fice daga dakin ya dauki system dinsa ya fara yi mata processing visa! *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (50) ***A zaune Mama take kan ta yayi masifar daukar zafi, ta rasa yadda zata bullowa al'amarin gashi dole ba zata karyata Nafin ba ta zabi Tariq, tasan ba zai aikata ba, bata so kuma maganar ta kai wajen Baba dan tasan dama a ciki yake da ita, kuma zai ce menene dalilin tura yaran gidan Tariq din. Dakin da Nafi take ciki da Salmar ta tashi ta shiga, ta same su sun yi jingum jingum. "Magana zamuyi Nafi." "Maganar me Yaya? Bayan kin goyi bayan danki saboda ita Salmar ba taki bace ba." "Ba haka bane ba, ban goyi bayan sa ba amma kuma ina tantamar Tariq da aikata irin wannan laifin, duk da an ce ba'a shaidar d'a." "Dama a duk irin wannan abun mace ake cuta, yanzu shikenan haka za'a bar maganar? Ni da ban zafafa ba idan ma hakan ne ai shi sai ya aureta tunda shine ya fara bata ta." Runtse ido Mama tayi maganar na shigar ta kamar an soka mata mashi, girgiza kai tayi ta karaso ciki ta zauna sosai tana kallon Salma "Da yaushe da yaushe ne hakan ta faru? Kuma ke kadai ce a wajen ko tare kuke da Amira?" Kallon uwarta tayi sai kuma ta kalli Maman "Tun anan gidan ne." "Yanzu me kike so ayi Nafi?" "MU rufawa juna asiri, ki saka Tariq ya auri Salma kawai, kinga shikenan mun rufe asirin juna tunda dai ai uwa daya uba daya ba wasa bane." "Shikenan, zan masa magana." Sai ta mike "Mu bar maganar a tsakaninmu dan Allah, har zuwa lokacin da zamu samu bakin zaren." "Ba matsala." Fita tayi ta ja musu kofar, da sauri Salma ta tashi ta rungume Aunty Nafi tana kyalkyala dariya "Ke da kin tsaya sokwanta, ina neman miki inda zaki huta kiji dadi, Allah na tuba gida be koshi ba zaa kai dawa ne? Itama Yayar duk da ita amma dama ina kai ina bari kishiya ta mallake ma da, in dai Tariq ya aure ki Jidda ta zama sorry wallahi, dan sai mun kore ta da kafarta" "Allah Mami bana son yarinyar nan,." "Ni kaina ba sonta nake ba,amma tunda uwar Tariq zata sashi auren ki ai dole ma ta tattara tayi gaba dan kin ganni nan? Bana zama da kishiya kuma ban taba bora ba, shi kanshi Babanku da matar sa na same shi amma wallahi da kanta ta nemi saki tayi gaba, ba zata iya ba." "Yanzu Jiddan ma zata tafi?" "Dolen ta, ai barewa ba zatayi gudu dan ta yayi rarrafe ba, duk abinda ake dan su wa ma tukunna ake yi? Dan 'yaya ne dama." "Shiyasa nake son ki Mami na." "Ki saki jikinki kamar anyi an gama, sannan ki cigaba da acting din da nace miki dan hankalin Maman ya cigaba da tashi, idan yaso kinga zata fi daukar mataki dan tana tsoron magaanar ta kai wajen Baban." "zan cigaba kuwa." "Good, haka nake son ji." Da sauri Mama ta bar jikin kofar bayan ta gama jin komai, dama chan bata yarda da maganar ba dan tasan halin Nafi sarai zata iya shirya komai, kuma dama bata taba sha'awar Tariq din ya auri Salma dan sak halin uwarta take dashi, duk da bata son Jidda amma a yanzu sai take jin gwara Jiddan sau dubu akan Salmar.     Zama tayi tana tunanin mafita, sai ga Fauwaz ya shigo, dakin ta suka shiga ya zauna sannan ta karanta masa komai da taji. "Mah wai dama kin yarda ne?" "A ah Fauwaz, kawai bansan wanne irin tunani zanyi ba." "Toh wallahi ko kaffara ba zan ba Ya Tariq ko kallo bata ishe shi ba, bare har akai ga haka, kawai dai sharri suke son masa, muka mah ba dan ke ba nasan Ya Tariq sai ya rufe su wallahi." "Naga yadda ransa ya baci sosai wallahi, shiyasa da yace su fita nace muje dan nima zama na bashi da amfani." "Amma me yasa bakya son Jidda Mama? Wallahi Jidda bata da matsala kuma nasan zata chanja Ya Tariq fiye da yadda muke tunani,." "Kawai bana son ta ne, a bar maganar." "Yanzu toh me ya kamata ayi?" "Nasan me zanyi." "Shikenan, Umaima ta kira wai aakai mata wasu kayan ta." "Eh Amira ta fada min, sai suje anjima da Maryam driver ya kaisu." "Ok." Wayar ta ce tayi kara Fauwaz dake gefen ta, ya miko mata. "Baba ne, ko sun sauka?" Tace tana daga wayar. Gajeriyar magana sukayi yace yana daf da shigowa gidan, tashi tayi tabi ta kofar baya zuwa shashen shi kuma Fauwaz yayi relazing a cikin kujerar yana karo volume din TV. Salma ce ta fito tazo ta zauna tana kin kallon sa, tashi yayi ya zauna yana ajiye wayar hannun sa a gefen sa "Amaryar Ya Tariq." Da sauri ta waigo ta kalle shi, ya kashe mata ido daya yana dariya "Ashe kinsan sunan ki, sunan kuma yayi daidai dake fa." "Ya Fauwaz banda tsokana." "Kai I'm serious fa, Amma kinsan me?" "A ah sai ka fada." "Ki kyale shi kawai ki dawo kaina gani handsome guy ga naira gani single." Tsuke bakin ta, tayi ganin kamar raina mata wake son yi "Allah kuwa, gwara ki kama saurayi kamar ni bashi da yake da mata ba, kuma wallahi baya son ki..." "Kuma ba zai taba son ki ba, kinsan mu maza mun fi son mace me aji ba wanda take tura mana kanta ta karfi da yaji ba, sam ba aji bare daraja! Darajeless wallahi." Ya sake fashewa da dariya, cika tayi fam ta kasa bude baki bare ta maida masa, mikewa yayi yana tattare key din sa da wayar sa ya zo gaban ta ya karkad'a mata key din a fuska "Duk sanda kika shirya ki tura application dinki zan duba naga ko zan iya manage." Tana kallo yayi ficewar sa daga falon, ta tashi da sauri ta shiga ciki kuka na taso mata, kukan bakin cikin da ya guma mata kuma ta kasa bude baki ta rama. Wajen Yaya yayi wucewar sa ya sameta kamar ko yaushe tana kulla lalle a kafarta, jan kafar yayi ta kai masa duka da hannun da yake daure da leda da tsumma. "Jairi.", "Ni dai idan dan ni kike kunshin nan na yafe wallahi, nafi son kafar taki a haka a dan ya mushe." "Sai dai kafar matar kace a yamushe ba dai tawa ba." "Ina da wata matar ne bayan ke gimbiya?" "Uwar gimbiya, munafuki ai naji abinda kaje kana yadawa wai naje gidan Jidda Tariq ya wulakanta ni." "Ni? Waye ya fada? Karya ake min." "Kai tafi chan, ai duk abinda kaje kana cewa ya dawo kunne na tas!" "So dai ake a hada MASOYA biyu, ki cire lallen nan kizo muje gidan Ya Tariq din muci girkin amarya, sai na barki ko kwana biyu kiyi dan naga alamar kina son zuwa." "Allah ya tsare ni da zuwa gidan nan,marasa kunya kawai, kai ma ko auren kayi bani ba gidan ka." "Toh ai bani da wata matar bayan ke." "Mutan garin ku Fauwaz." Baba yace yana shigowa, sosa keya ya hau yi ya durkusa ya gaida Baban ya amsa yana murmushi, "Ka raina min uwata ko? Toh kaima sai an raina taka." "Ba haka bane Baba." "Ai wannan yaron ya maida ni kakar sa wallahi." "Rabu dashi Yaya, yaran yanzu ne sai hakuri." "Ko da yake ai gwara shi, shi wanchan da naje gidan sa ai kora da hali yayi min." "Wai Tariq?" "Shi fa, daga shi har Jiddan ashe fitsararru ne ban sani ba, jiran ta nake ai tazo har nan ta samen, taji maganganu wallahi." Murmushi kawai Baba yayi yace "Yaya kenan, Ina wuni, mun same ku lafiya?" "Lafiya lou wallahi, ya hanyar? Hankali yayi gaba ashe ko gaisawa bamuyi, gashi ba hannu bare na miko ma ruwa." "Karki wahala ma Yaya, tun safe muka dawo wani abun ne ya rike mu." "Toh Masha Allahu, Allah dai ya bada sa'ar abinda ake nema ya raba ku da makiyanku lafiya yasa a gama lafiya." "Amin Amin Yaya, addu'ar kenan." ***Tana nade a cikin blanket ya dauki towel ya daura a kugun sa fuskar sa fes gaba daya bacin ran da yake ciki ya neme shi ya rasa,sai farin ciki da ya mamaye ilahirin zuciyar sa. Jidda ta biya shi har da kari dan duk hasashen shi baya taba hasaso hakan sai yau da ya tsinci kansa a cikin duniyar Jiddan me cike da abun mamaki. Takowa yayi ya tsaya a saitin kanta ya dan runkwafo ya shafi gefen fuskar ta da hannun sa ta maze taki ko motsawa. "Nace fa i'm sorry ba zan sake ba." Muskuta jikin ta tayi,taki kallon shashen da yake, murmushi yayi ya sa hannu zai yaye bargon ta rike gam tana bud'e masa idon ta "Muje na miki wanka." "Ni bana so." Tace kwalla na biyo gefen fuskar ta, dan ba karamin wahala tasha ba sai tace ma yafi mata first time din wahala "Karki zama raguwa mana, tashi kinji? Na daina ba zan kuma yi ba." "Ni ka daina kulani." "Toh tashi ki yi wanka ki rakani wajen Baba, if not aka tambaye ni zance kina gida kina kuka dan nayi..." "Na shiga uku, naji toh zan tashi, ka tafi." "Um um, nayi googling yadda ake so kuyi, let me help you kar azo a samu matsala, dan bana wasa da wannan sweet place din." Ya karashe yana dage mata gira daya ya lashi gefen lips dinsa, juyar da kanta tayi mamakin rashin ta idon sa na sake cikata "Wai dama kana magana sosai?" Ta tambaye shi bayan ta sauko da kafafuwanta jikinta a nannade da blanket din. Dariya tambayar ta bashi dan shi kansa yasan yayi baki idan yana tare da ita, dan murmusawa yayi k'adan ya kama hannun ta ya mikar da ita, ta danyi kara kad'an yayi saurin jawo ta jikin sa. "Menene?" "Kafata ce take min ciwo." "Sannu, lets take our bath sai na miki massage." "Ka fara yi sai nayi." "Tare zamuyi." "Eh???" "Yes! Sunnah ce, Manzon ALLAH (SAW) ya kasance yana wanka tare da matan sa (Allah ya yarda dasu.)" Shiru tayi jin irin misalin da ya kawo wanda bata isa ta ja ko ta noke ba. Kama blanket din ya yi ya cire ya daura mata dan karamin towel iya cinya ya sakata a gaba har toilet din. Da kansa ya hada mata ruwa da dan salt kad'an yace ta shiga shi kuma ya tsaya gaban sink ya dau brush ya soma brushing bakin sa. Bata da yadda zatayi haka ta shiga duk da dama jiyan ma ta shiga dan babu abinda aunty bata fada mata ba tun kafin ma ranar, kuma har text message sai da tayi mata ta sake jaddada mata. Kusan 15mint ta dauka a ruwan sannan ya taimaka mata ta fito ya jata cikin whirlpool bath tub da ya cika musu da ruwa, idon ta a rufe duk kunya ta hanata sakat amma shi kamar ko a jikin sa, haka suka shiga tare tana nokewa tana komai amma ya hanata katabus, cikin wani irin salo ya dinga tafi da ita, ta kasa hanashi dan sosai take karbar sakonnin da yake aika mata. Kamar yadda da jini yake bi ya kai sako zuwa kwakwalwa haka sakon sa ya dinga zuwa matar har chan cikin kanta. Kusan minti talatin suka dauka kafin ya fito da ita tamkar karamar baby, ya ajiye ta sannan ya taimaka mata ta ya shirya ta cikin riga da skirt na atamfa shi kuma yasa wani yadi me laushi ya dora hula shigar da ba kasafai yake yin ta ba, kuma ba karamin fito da ainhin kyawun sa take ba. Tana zaune tana admiring abin ta, tasan kawai ALLAH ne ya bata ba wai dan ta kai matsayin ba, amma ta ko ina Tariq din lamba daya ne, duk da ko dazu sai da ya kara jaddada mata how lucky he is to have her amma kuma tasan ita ta fishi zama lucky din, kawai dai shi namiji ne shiyasa. Mayafi ya dauko mata da handbag tunda ya hanata yin komai, ya yafa mata da kansa dan hatta gashin kanta shi ya gyara mata shi ya saka mata wayar ta a handbag din ya rike sannan yace su tafi. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (49) ***Yana cike application form din ta fito tasha doguwar rigar material yellowish brown (Tan) ta rufe kanta da dankwalin ba tare da ta daura ba, dagowa yayi ya kalle ta, itama shi take kallo tana so taga yanayin da yake ciki, fuskar sa a tsuke take kamar dazun sai dai dan kad'an da ya saketa.   "Ina passport dinki?" Yace yana maida kansa k'asa ya cigaba da danna system din "Yana gida." "Wajen Aunty?" "Eh." "Ok come here." Ya nuna mata gefen sa da hannu, zuwa tayi ta zauna idon ta na kansa amma shi system din kawai yake kallo ga dukkan alamu abinda yake me muhimmanci ne a gare shi. Tsaki yaja ganin ana bukatar marriage cert shine kawai zai dakatar dashi, skipping wajen yayi sai da ya kai karshen page din sannan yayi saving ya ajiye system din yana juyowa ya kalle ta "Babu abinda yake miki ciwo?" "Um um babu, jikina ne kawai yake mun ba dadi." "I'm sorry kinji? Ba zan kara ba." Juyawa tayi da kanta yayi murmushi kad'an ganin ya bata kunya yace "Zan kara amma sau daya I promise." Juyowa tayi da sauri,ya gid'a mata kai "Sau daya kawai fa." "Bani da lafiya fa." "Toh na fasa, sai kin warke ko?" "Eh." "Good girl!" Ya shafi gefen fuskar ta "Dauko Hijab dinki ki rakani." "Gida?" Tace da yar murnar ta "A ah, wani waje." "Ok." Ta tashi  ta shiga ciki shi kuma ya wuce dakin sa, ya chanja kayan sa ya fito rike da wayar sa yana dialing number Madaki. Fitowa tayi ya riko ta yana manna ta da gefen sa, yasa hannu ya sakalo kafadarta yana daga wayar . "Hello!" "Hello Captain, kwana da yawa?" "Alhamdulillah Wallahi, ya aiki?" "Fine Alhamdulillah, akwai labari ne?" "Yes wai marriage cert nake so pls, and it's urgent." "Oh toh ai ba matsala,zaka iya shigowa yanzu?" "Yes yes, sai muzo ai." "Ok, ina 3rd floor idan kun shigo ciki just call me." "Alright! Gamu nan." "Sai kunzo." "Aha! Thank you." "Muje ko?" "Owk."  To soma tafiya a hankali, tsayawa yayi yana bude bakin sa ganin tana tafiya kamar toddler, dan yatsan targaden ya kalla yaga har lokacin da sauran sa. "Zaki iya tafiya kuwa..?"  Yace showing his concern kamar ba shine ya manta da targaden nata ba jiya "Zan iya." Tace tana kokarin daidaiwa "Anya? Let me carry you kawai." Ya matso yana riko ta kamar zai daga ta "Allah zan iya." Ta janye tana murmushi dan tasan tsaf zai aikata "Ok ok, muje toh." Ya bata hanya ta wuce ya bi bayan ta yana kallon step din ta daya bayan daya a hankali Fitowa sukayi Faisal na hango su ya taso da sauri, ya jawo motar zuwa in da suke tsaye, bud'e mata kofar yayi ta shiga sannan shima yabi bayan ta ya zauna a kusa da ita, sannan Faisal din yaja motar.    Shiru ne ya ratsa motar, duk yadda yaga ga kokarin ganin abinda ya faru be dame shi ba, ya kasa sam, baki daya ransa a dagule yake ya rasa me yake masa dadi, daurewa kawai yake dan baya so Jidda ta damu amma deep down zuciyar sa tafasa take. Ko kaf matan duniyar nan sun kare ba abinda zai yi da Salma, shi da yake da mugun choice ma ba komai ne yake masa ba, bare ita da bata da mara ba da katon gardi a gabansa, shine har zata iya masa wannan sharrin, bayan shi tunda yake ma be taba ko kama hannun mace ko kannen sa mata ba idan ba Jiddah ba, ita ma kuma dan yasan halilin sa ce, amma shine har zata ce yana taba ta which idan ya fahimta suna so suce tabawa as in having sex.   Dafe kansa yayi jin wani irin bacin rai na sake taso masa, ba dan alakar da ke tsananin su ba, babu abinda zai hanashi rufe su daga ita har uwar tata, amma ko a yanzu ba wai ya hakura bane, dole sai ya dau mataki. Kawai dan dai duk abinda zai biyo ta bangaren Mama baya taba kokarin ketare shi, shiyasa a dazun ma suka ci darajar ta.   Tunda suka shigo motar take satar kallon fuskar sa be sani ba, damuwar sa ta dame ta matuka musamman da ba taba ganin shi tayi a irin wannan yanayin ba, juyowa yayi suka hada ido ta marairace masa fuska kamar zatayi kuka, hannun ta dake cikin nasa tunda suka shigo ya shiga murzawa a hankali kafin ya jawota baki daya jikin sa.    A harabar wajen Faisal yayi parking, ya daga kansa yana kirga floors din sai ya ciro wayarsa ya kira Madakin sukayi magana yace gashi nan. Bud'e kofar yayi yace ta fito shima ya fito ya zagayo ya gyara mata Hijab din ta sosai sannan ya rike hannun ta "Ba zamu dade ba, marriage cert kawai zasuyi mana mu koma gida." Gid'a masa kai tayi yayi murmushi kad'an ya maida kallon sa wajen Madaki da ya sakko yake nufo su, "Oga da kansa." Ya mika masa hannu suka gaisa ya kalli Jidda kad'an "Ina wuni?" Ta gaishe "Lafiya lou amarya, ya gida?" "Muje ciki ko?" Tariq yayi saurin shiga maganar ya katse mata hanzarin amsawa "Muje toh." Yayi gaba suka bi bayan sa, yana tafiya da ita a hankali. Lift suka hau zuwa office din madakin, ya zauna bayan ya nuna musu wajen zama sannan ya fito da takardun ya mika ma Tariq din da pen, ya cike ya mika masa, sai ya ciro cert din ya cike komai ya bashi sukayi signing sannan ya fita zuwa wajen da suke printing ya bada akayi printing nasa out bayan shima ya saka hannu da stamp akai, wajn witnesses ma aka saka hannu cikin kankanin lokaci aka gama komai abinda yake iya kai 3days ma wani lokacin har sati ko fiye. Suna zaune ya dawo ya mikawa Tariq brown envelope yace "An gama oga." "Haka da wuri? Thank you so much." "Haba haba! Ba komai wallahi." "Nagode sosai." Ya mika masa hannu "Bari mu koma." "Shikenan toh, sai na jika. Fauwaz yace min ka kusa wucewa ko?" "Eh in sha Allah." "Ok Allah ya bamu sa'a baki daya." "Amin." "Amarya? A gaida gida." "Mun gode." Tace a hankali Suka fice ya girgiza kai yana murmushi, Tariq ba zai taba chanjawa ba, shi be ma yi tunanin Tariq zai yi aure nan kusa ba ma, kuma to a very young girl haka, irin su dama Allah yafi kama su wallahi. Dariya ya sake yi ya cigaba da aikin da yake yi kafin zuwan su.      Gidansu suka wuce ya kira Fauwaz tun suna hanya yace yaje wajen Aunty ya karbo masa passport din Jidda da important takardun ta ya jirashi a compound din gidan zai karba. A compound din suka same shi yana tsaye yana jiran su. "Ba zamu shiga ba?" Ta tambaya ganin ya rike ta bayan motar ta tsaya "Eh." Yace daidai lokacin Fauwaz ya karaso , ya sauke glass din ya karbi documents din sannan ya rufe yace su tafi. Shiru tayi bayan sun sake daukar hanyar gidan su, ta tabbatar akwai babban dalilin da ya saka shi hanata shiga gidan, tunda taga sanda ya tsuke fuskar sa bayan sun shiga gidan nasu. Wayar sa ce tayi kara ya dauka ganin number Baba ya sashi saurin dagawa "Tariq." "Baba barka da rana." "Barka dai, kuna lafiya?" "Alhamdulillah." "Toh Masha Allah, ya shirye-shiryen tafiyar? Duk da ma dai mun dawo muna nan Villa, so nasan zamu hadu kafin ka tafi sai muyi maganar." "Dama jiran dawowar ka nake Baba, na dan chanja shawara ne." "Toh ba laifi, mecece shawarar?" "Dama so nake mu tafi da ita." "Ita? Wa?" "Um.. Jiddaaa." "Toh! Toh shikenan, hakan ma yayi ai." "Nagode Baba, sai dai kuma..." "Ina jinka?" "Maganar Visa din? Zaa iya processing dinsa a cikin satin?" "Ba damuwa, kayi applying kawai sai ka fada min idan ka yi, ko a samu agent yayi applying din?." "Na ma kusa gamawa." "Toh shikenan, sai ka shigo da daddare in sha Allah." "Nagode Baba, Allah ya kara girma." "Amin ya Allah, Allah yayi muku albarka." "Amin ." Ya amsa yana jin nutsuwar zuciya, Baba ne kawai yake fahimtar sa, har ya saka masa albarka a komai. Mafiya yawan lokuta mata suna mantawa da wannan tsohuwar kalmar ciwon 'ya mace na 'ya mace ne a duk lokacin da wani abu ya hada su da mace yar uwarta da bata da wata alaaka da ita,musamman a bangaren aure sam basa daga kafa sai su futtuke su murje idon su kamar ba mace bace yar uwarsu kamar yadda suke yawan ikirari, duk da dai ma yanzu zamani ya chanja an daina fadin ciwon 'ya mace na 'ya mace ne sai dai a barshi a ciwon mace na namiji ne dan su suka fi fuskantar wadannan halittun duk da suma watarana idan suka botsare musu basa gane kai ko kafarsu.     Taimaka mata yayi ta fito ya kwaso takardun suka shiga ciki. A falon farko ta cire Hijab din ta wuce kitchen dan dubo Godiya shi kuma ya shige ciki. Bacci ta sameta tana yi a dakin ta sai ta juyo kawai tazo ta dauki hijab din ta wuce ciki. Daga toilet ya fito fuskar sa a jike, ya nannade hannun rigar sa zuwa damtsen sa da yake a cike. "Yi alwala muyi sallah." Yace yana daukar sallayar ya shinfida, wuce shi tayi taje tayo alwalar ta same shi yana goge fuskar sa da dan karamin towel, mikewa yayi ganin ta fito ya hau kan sallayar ita kuma ta zura Hijab dinta tabi bayan sa. Juyowa yayi gaba daya bayan sun idar ya dora kansa a saman kafarta ta waro ido tana kallon gashin kansa, lumshe idon sa yayi yana so ya sake samun nutsuwa. Bata hanashi ba, ta cigaba da kallon gyararren gashin kansa da yake ta sheki a kwance yayi layi layi, hannun ta, ta kai ta shafa kan nasa a hankali, da sauri ya bud'e idon sa ya daga kansa sama ya kalle ta,tayi saurin janye hannun ganin yadda yake kallon ta idon sa a lumshe sun shiga ciki sosai "Cigaba plsss karki daina." "Na'am?" "Yes! I love it." Kasa daga hannun tayi duk kunyar sa ya kamata, kamo hannun nata yayi ya dora akan nasa yana maida idon sa ya rufe ruf. Bata da zabi illa ta cigaba da shafa masa kan har zuwa wajen keyar sa, wata iriyar kasala ce ta kamashi, be san cewa kan nasa zai zama weak point dinsa ba sai yanzu, ji yayi yana neman loosing control, sai ya riko hannun nata da hannuwan sa biyu ya mike zaune yana jawota jikin sa. "An samu matsala." Ya rad'a mata a kunne yana kankame ta, ya shiga sniping wuyan ta zuwa saman habarta. Tsananin tsoro ne ya bayyana akan fuskar ta, hannun sa ya kai saman eye lashes dinta ya rufe mata idon yana sake rad'a mata "I promise to be a gentle man." Da sauri ta janye jikinta tana kokarin tashi, wane irin gentle man ana zaune kalou? Yasan kuwa yadda take ji? Hanata tashi yayi ya rike ta k'akam, duk ita ta jawo shi wallahi bashi da niyyar zuwa again, ita ta kunna shi, shi kuma ba zai iya resisting ba. Tsoro ne ya shigeta ganin da gaske yake ba da wasa ba. Haka dama auren yake? "Wayyo na shiga uku Baffa na." Tace jikin ta na rawa kaamar mazari, dagata yayi daga rikon da yayi mata, yayi musu masauki akan gadon yana rufa mata jikin sa baki daya, ya tsura mata ido yana bin kyakkyawar fuskar ta da kallo. Saman idonta yayi kissing kad'an yana kara hango zallar tsoro da firgici cikin idon nata. "Jiddanah." Ya kira ta da wata irin murya, kin amsawa tayi dan bata da bakin da zata iya budewa gaba daya ya dora mata nauyin sa ya hanata ko da motsi ne "Calm down and take a deep breath, ba abinda zan miki I promise." "Zaka daga ni?" "Eh in dai kika nutsu ba." Ajiyar zuciya ta sauke ta bud'e idon ta kad'an ta kalle shi, tayi saurin maida idon ta kulle tana jan numfashi "Zan hakura on one condition, idan kin amince." "Me?" "Tashi ki cire wannan rigar pls." Ya daga ta yana zama a gefen gadon "Dan Allah kayi hakuri wallahi zan mutu." "Ba abinda zan miki fa, so nake kawai ki chanja ta, tayi zafi da yawa plus bana son ta, ko kuma na cigaba.." "A ah zan." Tace ta mike tana ganin kamar ba Ya Tariq din da ta sani ba, kamar wani daban ne aka chanja mata shi. Kallon jikin ta yake har ta sauka ta nufi wajen kayan ta bud'e closet din ta tsaya tana kallon jerin kayan. "Zaki iya barin inners kawai it's ok." Yi tayi kamar bata ji shi ba, ta cigaba da daddaga kayan tana jan lokacin, yarfe hannun sa yayi ya mike ya karaso wajen tayi saurin jawo wata atamfa doguwa ya rike hannun yana bata fuska "Ni ba wannan ba." "Wacce toh?" "Let me see." Ya zura kansa ta jikin ta kamar me leke yana kallon kayan rabin kansa na jikin chest dinta, idon sa ne yakai side din da underwears din ta suke a jere, hannu ya kai zai dauki bra da pant tayi saurin tareshi, murmushi yayi ya matsa baya yana folding hannun sa har lokacin idonsa sun yi kasa sosai yana kallon ta "Ni su nake so ki saka kawai." "Innalillahi." "Yes! Ko na cigaba da fushin da nake yi, kuma sai na kara wannan abun." "Ya Tariqqqq dan Allah." Ta marairace zatayi kuka "Ya me? Say it again please, ban taba jin kin fadi suna na ba. It sounds really really good and sweet!" Kin fada tayi yayi murmushi yana taune k'asan lips din sa "Oya ina jira." "Bani fa da lafiya." "Na sani ai, shiyasa nake so kiyi feeling comfortable, wannan kayan sun yi nauyi da yawa." "Ni basu min ba." "Toh ni sun min!" Turo baki tayi, ta dauko wata riga da palazzo pants, ta nufi hanyar toilet yayi saurin shan gabanta "Ba za'a sake zuwa toilet chanja kaya ba, ai i'm not a stranger anymore." Juyowa tayi tana tura baki ta dauki Hijab ta saka akan kayan sannan tayi unzipping rigar ta ciki ta sauko k'asa. Karaf ya rike mata Hijab din yana dariya "Ni zaki ma wayo?" "A ah ba wayo zan maka ba." "Toh bari kiga yadda ake yi." Ya hau kicin-kicin zare mata Hijab din ta rike kam tana girgiza masa kai, rike ta yayi a jikin sa ya karasa zare Hijab din ya zama daga ita sai undies din, da sauri ta rukunkume shi ta chusa fuskar ta a tsakanin kirjin sa wata iriyar matsananciyar kunya na lullubeta hade da tsananin tsoron abinda zai iya aikata mata. Ji tayi ya daga ta sama chak, ya sumbaci saman lips dinta sannan ya nufi kofar barin dakin da ita, chusa fuskar ta tayi a kirjin sa taki dagowa har suka dangana da dayan dakin sannan ya dire ta yana kashe dukkan hasken dakin dama curtains din a rufe suke kasancewar masu kauri ne ya saka duhu ya mamaye dakin gaba daya sai dan haske kad'an. Rage kayan jikin sa yayi ya kwanta yana hade jikin su waje daya, ya shiga kissing din ta a hankali tun daga saman goshin ta har zuwa wuyan ta, cikin wani irin salo da ya kusan mantar da ita a wacce nahiya take, shi kansa yana daurewa wajn bin ta a sannu ne saboda tausayin ta da yake yi amma he's eager , so eager fiye da first time dinshi wanda shi kansa yasha wahala musamman da first time dinshi kenan, sai da ma ya wahala sosai kafin ma ya gane in da ake dosa gaba daya. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (51) ***Da kansa yake driving din hannun sa daya akan steering while dayan na rike da hannun ta dake saman kan gear yana murza shi a hankali. A haka suka karasa gidan da yake dan cike da mutane saboda dawowar Baban. Sai da ya shiga ciki sosai sannan yayi parking. Da dan saurin ta, ta kama handle din zata fita ya riko ta, ta juyo yayi kissing din lips dinta sannan ya cire mata lock din, murmushi me tsada ta sakar masa, ya maida mata sannan ta fita, yana kallon ta har ta shige ciki, kashe motar yayi ya fito yana saka bakin shade ya toshe idon sa. Da Usman ta fara cin karo ya dane ta yana kiran Ya Jidda. Da sauri Aunty ta fito sai ta tsaya tana kallon Jiddan cike da mamakin ganin ta "Wa nake gani?" "Aunty nice." Tace a kunyace tana rike hannun Usman din da yake cike da murnar ganin ta "Lallai sannu Tariq, shine ya sako ki a gaba kuka taho gida?" "Kai Aunty, ina wuni?" "Lafiya Lou, toh ai gaskiya ce, kwana nawa yau dududu." "Ai an daina irin wannan aunty." "Lallai, toh kuna lafiya dai ko?" "Eh aunty." Tace a dan kunyace tana tuna abubuwan da suka faru tsakanin ta da gogan nata "Ya targaden?" "Alhamdulillah, yayi sauki." "Masha Allah, Allah ya kara sauki, na zata ma fa gobe Tariq din zai tafi. Shiru kuma ban ga yazo ba." "Nima dai ban ga yana shirin tafiyar ba." "Ok kila ya d'aga, anma naga ya karbi passport dinki? Ko tare zaku tafi ne?" Ta dan bigi cikin ta, girgiza kai jiddah tayi "Nima dai ban sani ba, ranar dai yace min wai zan bishi?." "Sai kika ce a'ah?" "Ban ce komai ba." "Kaji sokuwa, me zaki zauna kiyi bayan zaman jiran sa da kikayi a baya? Sannan ke ba kin huta da kowa ba, ba'a ganki ba bare a kafa miki kahon zuk'a." Shiru Jiddan tayi, dan ita har hango tafiyar tasu take tare kawai dai bata son nunawa auntyn ne "Kin je kin gaida Maman Fauwaz din ne?" "A ah nan ya fara kawo ni, yace zai ga Baba ne." "Ok, sai kuje da Usman ki gaishe ta, Yaya ma tana nan tana jiranki, kun mata laifi wai." "Innalillahi, Hajiya Yaya." "Zakuyi mata bayani tana nan tana jan maganar dan sosai ranta ya baci wallahi." "Ni wallahi bani bace Ya Tariq ne." "Sai kije ki bata hakuri, dan shi kam dama sun saba." "Taso Usman ka rakani." "Bari na karasa shiryawa kafin ku dawo." "Ok." Tace ta kama hannun Usman suka fita bayan ta gyara yafen mayafin ta sosai dan ta lura baya so ***Wajen Mama suka fara shiga bata nan tana part din Baba, tana zaune bata ma san Maman bata nan ba Maryam ta fito da murnar ta sai ga Amira ma sun fito tare da Salma. Chak ta tsaya tana kallon Jiddan dake zaune suna magana da Maryam. Wani kululun abu ne ya zo mata makoshi, ta karaso tana yamutse fuska ta zauna a kujerar dake gefen su tana dauke kanta ta dauki remote tana kokarin chanja channel. Babu wanda ya kulata a cikin su duk sun rude da ganin Jiddan a ganin ta ma kamar sun kasa zama waje daya musamman Amira da take tsokanar Jiddaan da tayi fresh ta kara haske ita kuma tana cewa taji tsoron Allah. Tsaki taja wanda ya jawo hankalin su kanta, ta tabe baki tana kallo TV "An bi an ishe mu da ihu kamar yau kuka taba ganin ta." "Ina ruwanki?" Maryam tace tana hararar ta "Kinsan ta Mero, wai Ya Tariq fa take so ashe shine duk tasa wa Jidda kahon zuk'a." Gaban Jiddan ne ya fadi maganar ta dan tsorata ta, Amma sai ta daure tace "Ayya abun tausayi, ai Baby nawa ne ni kadai, ta gama haukan ta, ta hakura na tsare gaba na tsare baya." "Correct my girl." Maryam tace sai sukaa tafa da Amira suna kwashewa da dariya "Zan baku mamaki wallahi dukkan ku. Mtsw!" Ta mike sai gashi ya shigo, ita kadai ta ganshi dan su suna kallon ciki ne basa ganin me shigowa, kuma ta kofar baya ya shigo alamun daga wajen Baba yake "Allah nasan irin su Ya Tariq ba dai iya love ba, kinsa masu shiru-shirun nan wallahi hmm, bomb!!!" "Ba ruwana idan yaji ke kika sani." Tace tana musu dariya, Maryam ce ta karbe "Ai gaskiya ce ,Allah sa nima Salim dina ya iya soyayya, mu soye mu rakashe abun mu." "Amin wallahi." "Ehem ehem." Yayi gyaran murya yana gimtse fuskar sa, yaji duk abinda suka ce tun daga farkon hirar da Jidda ta kirashi da baby da kuma wadda suke yi yanzu, dadi daya yaji da Jidda tayi hankalin boye sirrin su, wanda mata da yawa yanzu suke bayyana sirrikan su ga kawayen su bayan haramun ne Allah ya hana. Diriricewa Amira da Maryam suka yi dan basu taba kawo zai shigo shashen ba, idon sa akanta tayi saurin sadda kanta k'asa l "Ya Tariq sannu da zuwa, ina wuni? A kawo maka ruwa? " Ko juice?" Maryam ta ce Duk sun rikice musamman da suka san ya ji komai da dukkan alamu "Munafukai." Yace a hankali, zamewa sukayi suka gudu ya zama daga shi sai Jidda sai Salma dake tsaye kaamar wanda aka dasa a wajen "Come here baby." Yace yana nuna mata gefen sa da yake zaune, pretending kamar be san da zaman Salma a wajen ba, wanda yake ji zai iya tashi ya jata har waje sannan yace securities su yi mata shegen duka ita da uwar ta. Har ba zata taso ba saboda kar Mama ta fito sai kuma ta tuna da Salma dake falon, tashi tayi a nutse ta isa wajen nasa maimakon ya barta ta zauna a gefen sa sai kawai ya dora ta akan cinyar sa, wani irin waro ido tayi tayi kamar zata tashi ya zagaye ta da hannun sa ya hanata tashin yana kashe mata ido daya "Maama?" Tayi kamar a hankali wanda shi kadai zai iya ji, yasan Mama ba zata shigo yanzu ba shiyasa ma yayi hakan. "Nayi missing dinki, so much." Yace yana saka hannun sa ya gyara mata lipstick din bakin ta yana kallon yadda lips din ta suke shining kamar yayi kissing dinsu. Da sauri Salma ta juyo yaji sanda ta bud'e kofa ta shige ya saki murmushi yana gid'a kansa. Yunkurawa tayi zata tashi again ya sake hana ta "Karki kara kokarin tashi idan bani nace ba." Kofar ce ta sake budewa sai kuma salati ya biyo baya da karfi, Aunty Nafi ce Salma na bin bayan ta "Tariq menene haka? Wanne irin rayuwa ce wannan?" Yi yayi kamar be ji ta ba, ya kusanto da bakin sa daf da na Jidda da kunya ta hanata ko da motsi ne, bata san dalilin sa nayiin hakan ba,ji tayi yayi mata peck a gefen kuncin ta, zuwa lips dinta na sama, yayi kamar zai hade bakin su waje daya da sauri Aunty Nafin ta tura Salma suka koma dakin ganin abin na Tariq yafi karfin tunanin ta. Cikata yayi ta tashi da sauri tana kin kallon sa,shi kuwa murmushii kawai yake idon sa a toshe da bakin glasses. "Kananan marasa mutunci." Yace a zuciyar sa yana relaxing sosai a saman kujera. Hanyar fita tayi ta dago ya kalle ta "Baby ina zaki?" "Wajen Yaya." "Ok bari na zo muje." Ya mike tayi saurin cewa "Dan Allah kar muje tare." "Why? Ke da babyn ki?" "Ni dai dan Allah." "Me yasa toh?" "Kunya zaka sa ni ji." Dariya yayi k'adan ya koma ya zauna "Shikenan sai kin dawo." Juyawa tayi ta fita shi kuma ya cigaba da zaman jiran Mama wadda ya baro su suna fafatawa da Baba akan abinda ya faru. **Kaamar munafuka haka ta shiga wajen Yayan tana labewa, Sarai Yaya ta ganta amma ta maze ta tsuke fuskar ta tana yin kamar bata ga Jidda ba "Assalamu alaikum." Tayi sallamar tana shiga gaba daya "Amin." Yaya tace a gajarce Kusa da ita Jiddan ta zauna ta kauda kanta gefe ta koma dayan gefen ta sake dauke kanta, "Dan Allah Yaya kiyi hakuri." "Da akayi me?" "Komai ma, dan Allah wallahi ba laifi na bane Allah Yaya, dan Allah." "Ba dai kin zabi miji ba? Ke dadi miji ko? Har kike rawar kai ki shige dakin miji da tsakar rana kiki fitowa ko?" "Na shiga uku." "Kiyi hakuri dan Allah." "A ah ai ba komai, ba komai kinji? Masu hali irin Malam ma kaza aji ya ka cika bare kana bin su, ni da zan siyar miki kima da darajar wajen sa shine kika watsan k'asa a ido kika shige daki kukayi mukus ko? Dadi aure " "Na shiga dari ma ba uku ba." Ya furta a hankali, sai kuma a fili tace "Ba haka bane Yaya, kiyi hakuri ni dai dan Allah." Noke kafardar ta, tayi "Dan Allah Yayarmu, Hajiya Yaya ikon Allah, ki taimaka kiyi hakuri ko na zauna na fasa komawa." "Ki zauna a ina? "Anan." "Kaji mukafukar yarinya, ni zaki ma kinibibi?" "Da gaske Yaya." "Wasa kike ko?" "Da gaske mana." "Toh ma hakura,." "Ni idan bakya so sai nayi zamana anan din kawai." "Nace miki na hakura, ba in da zaki zauna da ya wuce dakin mijinki, na bar maganar ma kwata-kwata, shikenan?" "Toh shikenan Yaya, amma da..." "A bar maganar, samo min yoghurt a firij na dan sha." "Hajiya Yaya da cin dadi." "Arzikin d'a, ke ma ki zage jiki ki zazzago su baka san wanda zai jikan ka ba." "Nawa ma kikayi Yaya?" "Sha hudu nayi." "Wai!" "Biyar ne suke raye a yanzu." "Masha Allah." "Haka mukayi haihuwar nan da wahala ma ba irin ta yanzu da gata yayi muku yawa ba, wai tsabar lalacewa wai da miji ake jego, mu zamanin mu ka isa? Ai kai da miji sai kayi arba'in har ba irin Malam masu bakin hali ba." "Zamanin ne ya chanja Yaya." "Ai na gani, sai a shige daka da miji a bar me zaman dabaro tana hamma da zare ido, yaran yanzu sam basu da ta ido wallahi." "Zamanin ne fa Yaya." "Ai sai ku karata ga ku nan gasu, shiyasa ni ba gidan wadda zanje zaman dabaro kin ganni nan, kowa ya karata chan." "Uhum." Jidda tace tana hasaso yadda zata kaya idan akace wai itace da ciki ko zata haihu. ***Fada sosai Baban yake ya dauki waya ya kira Tariq yace ya dawo, dama cewa yayi ya basu waje zai kirashi, sai gashi nan ya shigo ya kalli Mama da take cikin tsananin tashin hankali, ta so ita ta fara sanar da Baba maganar tayi masa bayani yadda zai gane amma sai akaci rashin sa'a ya sani wanda bata san ta wajen wa ba, amma kuma yace text akayi masa shiyasa tayi tunanin Nafi ce ta tura masa text din, bata san haka zata mata ba, gashi ta kara sata a matsala dan Baba yace babu ruwan sa tunda har ta iya tura Yara gidan Tariq din duk da tasan rashin dacewar hakan shima kuma ba zai iya komai ba illa ya tursasawa Tariq din auren Salmar kamar yadda yace Maman na so tunda da bata so ba zata fara tura su ba, babu irin bayanin da batayi masa ba akan Nafi karya take amma fafur yaki yace dama ai ya gaya mata tun ba yau ba, ta fita daga harkar gidan Tariq amma taki, shikenan tunda har ta zabi hakan dama kuma bata son jidda sai ya auri Salman dan ya gaji da halin ta. Gefen Baban Tariq ya zauna Baba ya kalle shi ya nuna sa da hannu sannan ya nuna Maman "Ga uwar ka nan, tasan duk abinda yake faruwa saboda son zuciyar ta, ta jawo maka matsala da kanta, bani da abinda kuma zan yi akan wannan maganar dan ko zuwa sukayi suka fadawa duniya sun bata min suna, babu kuma wanda zai yarda da mu, duk da su kansu illa zasuyi wa kansu babba amma mutane basa gane hakan idan har suka rasa abun da suka kwalla fa rai akai basu samu ba, toh sai su yi kokarin shafa maka bakin penti, yanzu zamani ne na social media kuma duk abinda aka ce siyasa ta shigo zakayi kokarin kare mutuncin ka da martabar iyalin ka dan abu kad'an sunan ka zai karade ko ina, bani da niyyar tursasa maka aure a wannan lokacin, amma tunda har ban isa na saka ko na hana mahaifiyar ka ba, shikenan gata nan,kaje ka fara shirye-shiryen auren Salmar, idan yaso sai ka ajiye Hauwa'u a gida kaamar yadda take so, ka dauki matar da ta zaba maka ku tafi" Da sauri Tariq ya dago kansa da yake duke, ya kalli Baban "Sai ka fara shirye-shirye dan babu lokaci, abinda mahaifiyar ka take so ne, tunda ita Hauwa'u ba 'ya bace a wajen ta,amma ta sani, tana da 'yaya mata duk abinda kayi wa dan wani kaima sai anyi wa naka." Kan Tariq a k'asa ya kasa motsawa dan be yi tunanin abinda Baban zai ce kenan ba, bayan yayi masa duk bayanin da zai masa kuma ya gamsu ya amince, amma kuma sai yaga Baban ya chanja baki daya kamar bashi ba, tashi Mama tayi dan tasan ko me zatayi ba zai saurare ta a lokacin ba, shiyasa kawai taga gwara ta fita zuwa sanda zai huce, sannan taje ta samu Nafi suyi duk wacce zasuyi dan wallahi da Tariq ya auri Salma gwara ta hakura da Jidda duk da bata son ta. Yunkurawa Tariq yayi zai bi bayan Maman bayan yayi godiya a ciki ciki Baban ya dakatar dashi yace ya zauna, zama yayi ya tankwashe kafarsa "Na kira wani a embassy, yace ku shiga gobe da safe, idan yaso daga chan sai ku wuce kanon." "Na'am?" "Eh, sannan akan maganar da mukayi yanzu..." "Baba dan Allah kayi hakuri wallahi ba zan iya auren yarinyar nan ba." "Na sani, kuma nima ba zan bari ka aure ta ba ,inaso mahaifiyar ku tayi hankali ne, ta ajiye duk makaman yakin ta,ta rungumi Jiddah dan idan aka tafi a haka ko 'yaya kukayi zata iya kin su, tunda tana kin uwarsu." Ajiyar zuciya ya sauke me karfi wadda har sai da ya bawa Baban dariy "Jairi, kannen ka mata ne suka sanar dani duk abinda yake faruwa tun ranar da uwata suka zo gidan, nayi shiru ne ina bibiyar komai,." _"Ashe yaran nan suna da rana."_ yace a cikin zuciyar sa, godiya ya sake yiwa Baban yayi masa sallama ya fito ya wuce kai tsaye wajen aunty dan yasan anan zai tarar da ita [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (52) ***Abinci ta zuba ta zauna tana ci a k'asan carpet suna hira da Aunty sai gashi ya turo kofar ya shigo bakin sa dauke da sallama. A ciki ta amsa Anty kuma ta amsa a fili tana masa maraba. Yanayin da ya ganta a zaune sai ya tuna masa ita ranar da ya fara ganin ta da muryar ta kamar usur wuyanta kamar mirikin lema. "Barka da rana Aunty." "Barka dai Tariq, ya gida?" "Alhamdulillah Aunty." "Madallah, ya shirye-shiryen tafiyar?" "Ana kan yi, Visa din Jiddah ce dama zata dan mana delay kad'an." Ya karashe yana kallon fuskar ta, tunda ya shigo ta daina cin abincin da take ci yana lura da ita "Masha Allah, toh Allah ya bada sa'a ya taimaka." A yadda Antyn tayi maganar zaka gane cewa ba karamin farin ciki tayi ba da tafiyar Jiddan, abinda dama take ta hangowa kenan dan indai ya tsallake ya tafi shikenan kuma kashin ta ya bushe a wajen Mama da Nafi dan ta lura Nafin ce take sake zuga Mama akan Jidda,yanzu kuwa idan suka tafi ba shikenan ba? "Bbyna..." Yayi maganar yadda aunty ba zata ji ba, dago kyawawan idanun ta tayi ta sauke su kansa, ya motsa bakin sa a hankali yace Kin gama?" Girgiza masa kai tayi ta cigaba da juya spoon din "Ok, ki karasa sai mu tafi." Gid'a masa kai tayi, yayi murmushi kad'an ya zare glasses din idon sa yace "Aunty, gobe zamu je embassy daga nan zamu wuce Kano in sha Allah." "Kai dama na biku kawai mu tafi wallahi." "Aunty mu tafi kawai toh mana." "A ah, babanku ma ba zai yarda ba, nima kuma tsokanar ku nake duk da inason zuwa din amma zan bari cikin next week in sha Allah." "Toh Allah ya kaimu." "Amin ya Allah.' Mikewa Jidda tayi da plate din dan babu kuma in da abincin zai cigaba da shiga dan gaba daya ya hanata sakat da kallon shi duk da idon sa yana cikin bakin glass amma tsaf ta gano kallon ta yake kuma ta san shi sarai zai iya bata kunya a wajen auntyn dan shi kam babu ruwansa ko a jikin sa. "Jidda dai wannan cin abincin na wasa me wallahi." "Shiyasa bata kiba ai aunty." "Aikuwa, a haka ma ai jiddah tayi kumari, sosai." "Yanzun ma da sauran ta." Yace k'asa-k'asa amma sai da taji, ta juyo ta dan kalle shi ya motsa bakin sa yana mata murmushi ta shige kitchen din ta wanke bakin ta sannan ta fito ta wuce tsohon dakin ta, bin bayan ta aunty tayi suka barshi a zaune tana shiga ta zauna tace Jiddan ma ta zauna, rike da hisnul muslim dinta da counter sai yar jakar da sarka da abun kafar nan suke ciki da ta dauka a cikin kayan ta tazo ta zauna kusa da Auntyn "Akwai abinda yake damun ki ne?" Ta tambaye ta tana kallon yanayin Jiddah da yadda take abu very cool duk da dama chan haka take amma yau sai taga ya karu. Girgiza kanta tayi "Babu komai aunty." "Akwai in da yake miki ciwo ne?" "Ba ko ina." "Toh na tura miki text tun ranar kin gani?" "Na gani aunty." "Yawwa, ki yi hakuri kowacce mace da kika ganta a haka ta fara, girman kenan, ke dai banda gardama dan ita ke jawo ma mutum matsala, dama dai chan kinga ba wasu uban magunguna aka narka miki ba, mafi a'ala dai shine maganin sanyi, idan aka kwana biyu da kanki zaki nemi karin wasu abubuwan ba sai wani ma yaji ba, yanzu dai ki daure kiyi hakuri na lokaci ne da ya wuce shikenan, ki gyara jikin ki da mijin ki sannan kiyi masa biyayya iyakar iyawar ki." "In sha Allah Aunty, nagode sosai Allah ya saka miki da gidan aljanna, ba dan ke ba aunty, da bansan ya rayuwata zata kasance ba, da nasan yanzu ina chan cikin wahala da tashin hankali, bani da abinda zan yi na biya ki Aunty." "Abu daya zakiyi ki biyani, duk runtsi duk wuya karki taba bijirewa mijinki, kiyi kokarin kyautata masa sannan ki sani, soyayya karamar abu ce a zamantakewar aure, kuma ita kadai bata iya dorar da aure, hakuri da addu'a sune babban makami domin akwai kalubalai masu tarin yawa da zasu taso miki, wanda zasu bude miki ido kisan mecece ma rayuwar." "In sha Allah aunty." Tace cikin muryar kuka, ita kanta tasan akwai kalubale sosai a rayuwar aure tunda taga yadda ita kanta Auntyn tayi hakuri kafin yanzu da komai ya wuce sai dan abinda ba zaa rasa ba, ta kuma ga yadda Baffan ta yasha wahala a wajen Iya Lami , sannan ga yadda Yaya a kullum take labarin wahalar da tasha a rayuwar auren duk da ba lallai dan abu ya samu wane kai ma ya same ka ba, amma idan ka sawa ranka Allah zai iya jarrabarka shikenan zaka zauna lafiya kuma cikin shiri. Hawaye Aunty take amma bata bari Jiddan ta gani ba, tasa bayan hannun ta, ta share sannan tace ta je su tafi kar yayi ta jira, zata aiko da sakon Baffa da zata tafi masa dashi. Tashi tayi jikin ta yayi matukar sanyi ta jawo mayafin ta har saman fuskar ta yadda ba zai ga fuskar ta ba har ya gane kuka tayi ba. Waya yake ta fito tana kallon k'asa, ya zura mata ido yana so ya gano wani sauyi a tare da ita, yanayin tafiyar ta ya nuna kamar she's down, katse wayar yayi bayan ya ciro ya daga kunnen sa, ya mike tsaya ya zura ta a aljihun gaban rigar sa, ya riko hannun ta yana leka fuskar ta, hawaye ya gani yayi a kwance a fuskar tata, yasan definitely wata maganar sukayi da aunty amma be san wacce ba, baya fatan tasan maganar Salma da abinda yake faruwa wanda yayi tunanin Auntyn ma bata sani ba, tsoro ne ya darsu a ransa kar dai ko auntyn ta sani shine ta fadawa Jiddan "Menene?" Yace ciki nuna tsantsar kulawar sa, gefe daya kuma yana jin tsoron amsar da zata bashi dan be san a yadda zata kalli abun ba, tunda yanzu ne ta fara sanin sa bare ta banbance abinda zai iya da wanda ba zai iya ba. "Ba komai." "Tom ki daina kukan kinji? Muje mota sai ki fada min menene." Da ka ta amsa masa, ya karbi yar jakar daga hannun ta ya rike mata dayan hannun suka fita daga falon. Motar na nan in da ya ajiye ta dan haka kawai bud'e mata baya yayi ya taimaka mata ta zauna sannan shima ya shiga da sauri, ya jawo ta baki daya jikinsa da yake motar tinted ce, kukan shagwaba ta saka masa ya rikice ya rasa yadda zai yi, ita bata san baki daya kukan ta rikita shi yake ba, kuma shine babban weak point dinsa, tapping bayan ta ya dinga yi a hankali har ya samu tayi shiru, ya zaro tissue daga saman dashboard ya goge mata fuskar bayan ya dago ta daga jikin sa "Menene?" "Ni Baffa na." "Kike so ki gani? Shiyasa kike kuka?" "Eh." Ta gid'a masa kai, ajiyar ya sauke da karfi jin ba waccan magaanar bace yace "Zaki ganshi gobe in sha Allah." "Sai me kuma?" "Babu komai." "Ok..." Ya zare jikinsa a hankali ya fito ya dawo mazaunin driver yaja motar suka bar gidan. ***Masifa aunty Nafi take Salma kuma na ta gursheken kuka, tsabar wulakancin abinda Ya Tariq yayi musu ace a gaban su sai dinga romancing matar sa, gashi wallahi ita da gaske take tsananin son sa da kaunar sa take kamar ta je ta shake Jidda har lahira, ita kanta Aunty Nafi taji haushin wulakanci da yayi musu ai ko ba komai ita matsayin uwa take a wajen sa, amma saboda wulakanci shine zai maida su yan iska yana rungumar mace a falon mahaifiyar sa. Banko kofar akayi Mama ta shigo tana huci kamar zakanya, tashi aunty Nafi tayi tana kallon ta da mamaki "Ki tattara yarki da tsummokaran kayan ki, ki bar min gida na, kuma wallahi wallahi Tariq ba zai taba auren Salma ba, tunda ke muguwa ce makira, baki duba karfin alakar mu ba, har ki kala wa dana sharri saboda kawai son zuciya." "Ban gane sharri ba, kina nufin Salma sharri tayi wa Tariq kenan, kuma kin goyi bayan sa?" "Eh sharri kikayi masa bakar muguwa, wallahi sai kin tafi bani ba ke kuma wallahi." "Ahayye! Tab Amma sannu Aisha, kina nufin zaki rabu dani akan danki? Yaran yanzu da ba shaidar su ake ba?" "Nayi, kuma kema kinsan duk abinda kuka fada akan sa karya ne, toh wallahi ko ku tafi da kafarku ko securities su fidda ku." "Aikuwa wallahi ba zai yiwu ba, a dake mu a hana mu kuka, ba za'a bata min yarinya kuma ace zaa kore mu ba, wallahi ba inda zamu ko Tariq ya karbi Salma ko kuma zance ya karada dukka kasar nan." "Idan kin ga dama ki dau loud speaker ki zaga kaf duniyar nan kina fada, babu abinda zai faru illa kanki da zaki WA illah, dan ko a yanzu babu me karbar yarki da wannan banzan halin nata ballantana son zuciyar ki yasa ki bata suna, kinga zata kare a haka ba aure." Mamakin yadda Maman take kokarin wargaza musu plan dinsu ya saka jikin ta sanyi, amma sai ta hana ta gane halin da ta shiga tace "Ai akwai hukuma ko? Wallahi sai naje sun bi min hakkin 'ya." "Kije binnin sin ma, kuma wallahi ko a hanyar gidan mu na chan Kano na sake ganin ki sai na saka an rufe min ke an jefar da mukullin." "Naji duk abinda kuke fada ke da yar taki kuma nayi recording din komai, dan haka sai a bi wani sarkin ,tunda baki san halacci ba." Shiru Aunty Nafi tayi ganin dai da gaske Maman ta gano plan din su, kenan ta ji maganar ko dai so take ta sakata fara feeling quilty? Juyawa Maman tayi ta fita, jim kad'an sai gata ta dawo da wasu masu aiki daga bq su biyu kedaru majiya karfi,suka shigo dakin tace su kwashe kayan su Anty Nafin su fitar mata dasu, tsoro ne ya shigi Anty Nafi, tana so tayi magana amma kuma tana tsoro dan bata taba ganin bacin ran Maman haka ba sai yau, dan komai akayi mata bata cika tankawa ba, shiyasa tayi tunanin zata iya amfani da wannan damar ta cutar da Maman ta kakabawa Tariq Salma ta samu hankalin ta ya kwanta. "Ba sai an mana wulakanci ba zamu fita." Tace tana yin wajen kayan, zata taba Mama ta dakawa masu aikin tsawa tace bata son jira su kwashe kayan, da sauri suka suri akwatin tasu sukayi waje, Salma babu ko mayafi akan ta sai wata hula ita kuma Aunty Nafi sai mayafi suka fito Maman na tsaye suka wuce, already tayi waya gate tace sam ya sauke su a tasha suna fita aka saka musu kayan a booth Salma sai kuka take Anty Nafi kuma ta kasa cewa komai saboda yadda ran ta yayi bala'in baci. Zama Mama tayi a nutse tana dafe kanta da yake mata kamar zai rabe biyu, bata san ta tara damuwa haka ba sai yau da Baba ya birkice mata, ta kuma san kafiya irin tasa shiysa ba zata taba amincewa ya aiwatar da abinda yayi niyya ba, da kanta zatayi kokarin ganin Tariq da Jidda sun bar kasar baki daya gwara su je su karata a chan duk da bata son Jiddan bata kuma san yaushe zata so ta ba amma gwara ita akan salma.da ta gama saida mutuncin ta a titi. Maryam ce tazo ta zaune a gefen ta, ta dago tana kallon ta sai ta girgiza kanta "Ya akayi? Zaku je gidan Safiyya daga nan ku wu kaiwa Umaima kaya." "Ok sai muje gidan Ya Tariq?" "Bana son neman magana." "Dan Allah Mama, ba zamu dade ba." "Toh naji, idan kunje KU gaishe su " "Har Jiddah?" "Ban sani ba." Tace tana jan tsaki "Wai Mama, Anty Nafi yar gidan ku ce itama Hajiya Babba ce ta haife ta?" Girgiza kanta tayi "Bamu da alaka ta jini ko kad'an, yar abokin Alhaji ce, zumunci irin na da da iyayen suka rasu shine aka bawa Hajiya Babba ita dan dama gida daya muke tun a dah, shine muka taso tare babu wani banbanci, amma kinga ai yanzu ta nuna min jini ba karya bane ko? Tunda na tabbata abinda tayi min Mimi ba zatayi ba, anyways, we learn from our mistakes, ya wuce in sha Allah." "In sha Allah." "Tashi kuje kar kuyi dare." "Ok ina kayan suke." "Suna cikin daki na, ki taho min da wayata na kira Dr Iman tazo tayi mun bp." "Ok mah." Ta wuce ciki ita kuma Maman ta kurawa waje daya ido tana tuna abinda ya faru. [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©®*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (53) ***Kusan tare suka shirya a gurguje saboda saura kiris su makara, tea kawai suka sha da slice bread suka fito Faisal ya dauke su zuwa Embassy din. Da zuwan su Alhaji Tahir ya fito har kofa ya shigar dasu bayan ya rike hannun Tariq din jidda kuma ta bi bayan su zuwa wani hadadden office. Zama Tariq yayi a kujerar dake facing ta Alhaji Tahir din ita kuma ta zauna akan couch din dake baya da dan madaidacin table a gaban wajen, fridge ya bud'e ya dauko musu ruwa da lemo sannan ya karbi takardun ya dan duba su kad'an ya mike ya fita bayan yace yana zuwa. Juyowa yayi gaba daya da kujerar suka hada ido ya dage mata gira tayi murmushi tana kallon kofar shigowa. "Sai na taso ma." Yace yana kokarin mikewa, da sauri ta hau girgiza masa kai "Dan Allah kayi zaman ka anan." Murmushi yayi ya girgiza kai, ya juya daidai lokacin Alhaji Tariq din ya dawo yace su taso, suka bishi ta wata kofa ba wadda suka biyo dazu ba, ya kai su wani babban office yace su shiga su zauna, suna zama Mr Biden ya shigo shima. Cikin kankanin lokaci suka gama abinda zasuyi suka fito bayan sun wuce layi me yawa a reception din wajen. Godiya sukayi masa yace su gaida Baba suka fito shi kuma ya juya zuwa ciki.      Jirgin rana zasu bi zuwa Kano, shiyasa sai da suka fara komawa gida suka karasa shiryawa, kwana Jidda take so tayi a gidansu amma taka take-taken Tariq din kamar ba zai barta ba, kwana biyu yace kawai zasuyi wai idan suka je kano yau gobe da wuri sai su tafi garin su Jiddan, su dawo da yamma, su sake kwana sai su dawo da next day, kaya ta dauka kusan set biyar incase ko zai chanja shawara ya barta, yana lura da ita da tana saka kayan a suitcase yayi kamar be gani ba dan be shirya barin ta ba, bayan yasan duk rayuwar da ta shiga a wajen Matar baffan ta, SANADIN LABARIN da ya saka masa tausayi da kaunar ta, tun ranar farko da ya fara dora ido akanta, ya samu kuma labarin ta, yake dawainiya da son ta shi kansa ba tare da yasan me yake ji ba, ya damu da ita sosai har ya zama yana tuna ta a kowanne lokaci har bayan tafiyar sa, dalilin da ya saka shi kiran Aunty a wanchan lokacin. Duk a tunanin sa tausayin ta kawai yake yi, shiyasa ya dinga chusawa kansa ra'ayi akan irin matar da yake so ya aura, yana kokarin dakushe zuciyar sa da nuna mata ai jiddah bata cikin wannan layin.   Tasowa yayi ta bayanta tana ciro undies dinta a bobboye dan kar ya gani tana turawa a cikin kayan nata. Rungume ta yayi tsam yana dora kansa a saman kafadarta, da sauri ta saki sleeping dress din da ta ciro zata sake chanja mata waje cikin wanda Aunty ta aiko mata, irin fitinannun sexy nighties din nan ne dan rigar ko kusa da zuwa waist dinta batayi ba, da kad'an ta kai saman cibiya sai wani transparent pants sannan rigar ta baya a bud'e take gaba daya. Yaga sanda ta yadda rigar, sai ya cikata ya duka ya saka hannu ya dauki rigar yana dagata, kamar wadda aka dasa a wajen haka tayi ta dauke numfashi tana rufe idonta sanda ya dauki rigar ya dagata yana kallon ta idon sa a shanye kamar wanda yasha wani abun, shiru taji yayi ta dan bud'e ido kad'an suka hada ido ya kad'a mata kai yana daga mata rigar "I love this." "Ajiya fa aka bani." Tace still idon ta a kulle. "Waye?" "Em.. Ami... Ya Safiyya ce ta bani ajiya." "Me yasa ta baki ajiya?" "Nima ban sani ba." "Shikenan ta zama tamu, zan biya kudin amma ba zamu bata ba gaskiya." "A ah gwara a bata mu ba abinda zamuyi da ita." "Ko? Mu ke da abinda zamuyi da ita ai, beside ko kyauta ne ma Sofy zata bani matata ta saka min na gani." "Innalillahi!" Dukawa yayi ya tura ta a suitcase din sannan ya rufe yana yin wani irin shu'umin murmushi sannan ya rufe yana daga su "Nasan in da ake saida irin su don't worry zan siya miki kinji?" "Ni bana so." "Allah sai kinso, tunda ni inaso." Turo baki tayi ya matso daidai fuskar ta yayi magana a hankali "Inaso na dinga ganin ki cikin lingerie and bikinis. I don't mind idan ma kika zauna haka, eh kin gane...." Ya kashe mata ido daya, da sauri ta juya tana kunshe dariyar ta. "Common... life din is too short let's enjoy our self Baby " Kin kallon sa tayi, ya koma ya zauna yana murmushi kasa kasa , ya dauki wayar sa ya kira Fauwaz yace yazo ya kaisu airport daga nan zai aike shi wani waje. Fita tayi daga dakin taki yarda ta kalle shi kwata-kwata shi kuma babu abinda yake sake birgeshi da ita irin kunyar ta.     Dakin Godiya taje ta sameta a kwance tace ta hada kayan ta za'a kaita wajen aunty zasuyi tafiya su, tashi tayi da yar murnar ta tunda dama mamanta tana aiki a gidan nasu ne shine aka bata yar, a gurguje ta gama hade kayan ta dauko kudi ta saka mata a kayan sannan ta dauki waya ta kira gate tace Faisal ya kai ta gida dan ta kira Aunty already tace ta turo ta tunda basa nan kuma ko sun dawo ma daga kanon tafiya zasuyi gwara kawai ta dawo tunda babu amfanin zama. Tana kokarin komawa ciki bayan yarinyar ta fita sai ga Fauwaz ya shigo, tsayawa tayi ya karaso ciki suka gaisa sai ta tuno babu ko mayafi a jikin ta, tasan kuma halin oga aka, ciki ta shiga ta bar Fauwaz din bayan tace masa tana zuwa, ta shiga dakin ta, ta chanja zuwa bakar abaya tayi rolling sannan ta same shi a dakin sa tace masa Fauwaz yazo. Tashi yayi ya fito bayan ya jawo suitcase din tasu ita kuma ta cire musu cable din wayar su ta dauki bottle water a fridge sannan ta saka abinda tasan zata bukata a cikin handbag dinta ta fito sanye da flat shoe. A tsaye ta same su daga Tariq din har Fauwaz din suna magana, tana fitowa Fauwaz yaja kayan yayi gaba shi kuma ya juyo yana kallon shigar ta kafin ya kad'a kai, babu wani aibu she looks decent dan yasan ma'aikatan wajen zasu iya kalle mishi mata ganin how beautiful she is amma a kalla if shigarta is ok ko sun kalle ta ma sun kalli Allah ya isa kawai. Shi a ganin sa ma fa Jiddan sa ta kai matsayin saka nikaf kawai saboda baya so taji ta a takure ko taga kamar ya matse ta shiyasa yaki cewa din amma wallahi da zata saka shi sai yafi kowa jin dadi, babu shegen da zai kalleta bare har yayi admiring kyauwun ta a zuciyar sa. Hannun sa ya sarke a cikin nata suka fito bayan ya karbi ruwan ya sha kad'an. Wani ne daban a mazaunin driver sai kuma wata mota daya da Tariq din be san ta ba, itama da mutum hudu a cikin ta, fitowa sukayi da sauri suka gaida Tariq din ya gansu wasu manya fuskar su a toshe da bakin glass gefen aljihun kowannen su dauke da bindiga "Ban gane ba." Yacewa Fauwaz bayan ya budewa jidda mota ta shiga, kad'a kai Fauwaz yayi yana dariya "Abokin Babana ya samo mana su wallahi, shi Baba baya so amma yaki yace yadda rayuwar nan ta zama wallahi tunda dai mun shiga circle din dole ne muyi abu kamar nasu, this two naku ne har ku wuce tare zaku tafi Kano din ma yanzu.".  Ya karashe yana dariya "This is serious, kenan mutum ba zai yi rayuwar sa ba haka nan sai da wasu? Waye ma ya damu ne wai damu ma?" "Haka kake gani fa, insecurity din ya wuce in da kake tunani, akwai wasu ma da zaku hadu dasu kuna sauka a airport." "Are you kidding me? Kai aka sani ai bani ba." "Allah I'm serious, muje kar kuyi missing flight." "Abun babba ne." Yace sannan ya shiga gefen Jidda shi kuma Fauwaz ya shiga gaba. ***A mintiunan da basu gaza awa daya suka isa Kano, suna sauka kuwa suka hadu da wasu zugar securities din suna jiran su, shi abun ma dariya yaso ya bashi, sai kuma dai ya share yace su kaisu chan main house din su Mama akwai abinda zai yi kafin su wuce masaukin su, sabon gidan da sukayi anan nasarawa gra. Zasu shiga motar kenan taji an kira sunan ta, tsayawa tayi chak muryar sa na dawo mata tar akanta. Ya Isma'il ne, "Jiddah."  Safeera ta kirata ta juyo da sauri idon ta ya sauka akan sa, yana cikin ashe colour din suit idon sa sanye da siririn medicated glasses fuskar sa dauke da murmushi "Safeerah,Ya Isma'il!" Ta fada a lokaci d'aya cikin jimla daya. Tsayawa Tariq yayi rik'e da murfin motar idon sa akan wanda aka kira da Ismail din da yadda yake kallar masa Jiddan sa. Hugging din Safeeran tayi sannan ta gaida Ya Isma'il din ya amsa yana matsawa ya mikawa Tariq hannu "Oga barka da rana." Kamar ba zai mika masa hannun ba dan sai da yayi dan jim kafin ya mika suka gaisa. "Safeera ce da brother din ta." Tace tana murmushi "I see!" Yace a d'age yana sake kallon  Isma'il din wanda yake ganin kamar tunda yazo wajen Jidda kawai yake kallo. "Muje ko?" Yace "Ok zan shigo na gaida Mom in sha Allah." "Ya dai kamata wallahi, Ya Tariq sai anjima." "Sai anjima." Ya maida mata "Ok sir, ku gaida gida, Jidda bye." Ya ware yan yatsun sa guda biyu ya dagawa Jiddan su "Ok 👌." Motar ta shiga sannan shima ya shiga ransa na baci sosai, haka kawai yaji baya son Isma'il din. "She's my best friend." Tace tana kallon sa da murmushi a fuskar ta. Nodding kansa yayi be ce komai ba,shiru tayi ganin kamar mood dinsa ne ya chanja. Tunanin yadda zasu kwashe da a gidan su Maman ta shiga yi. Bata san wacce irin tarba zata samu ba, shiyasa duk jikin ta yayi sanyi ga Tariq din ya gimtse fuska yaki yarda ma ya kalli side din da take.   Wayar sa ya zaro zai kira Ishaq yaga missed calls din Yasmin kusan kullum sai ta kirashi ko tayi masa message a WhatsApp, da gaske take ba zata barshi ba kila sai ta ganshi tare da Jidda sannan zata kyale shi. Fasa Kiran Ishaq din yai ganin an zo gate din gidan su maman.    Idon ta akan gate din ganin irin girman gidan bata taba kawo Maman daga irin wannan gidan ta fito ba duk kuwa da dama kana ganin ta kasan masu kudi ne amma bata kawo har haka ba, shiyasa Maman tayi mugun raina Anty dan ko kusa ba tsarar ta bace idan banda kaddarar aure babu yadda za'a yi su hadu inuwa daya.    Harabar gidan zata ci motoci kusan sha biyu saboda girman sa, ga motocin nan a faffake wasu lullube wasu kuma daga gani ba'a dade da hawan su ba. Fita yayi be ce ta fito ba sai tayi zaune tana tunanin ko ba fitowa zatayi ba, har yayi gaba sai ya juyo ya ganta a zaune duk da an bud'e mata kofar bangaren ta. Dawowa yayi da baya yace ta fito, ta fito tana satar kallon fuskar sa. Hanya ya nuna mata yace tayi gaba ya take mata har suka main entrance din. Door bell ya danna jim kad'an aka zo aka bud'e. Da sallama suka shiga dukkan su cikin falon da yake dauke da kujeru set uku saboda tsabar girman shi. Hajiya Babba na zaune a falon ta dago idon ta sanda taji sallamar kamar ta Tariq, shi din ne kuwa sai taga ya kara girma sosai. Al'amin ne yayi karaf din cewa "Wa nake gani kamar Captain?" Murmushi yayi wanda ya tsaya iya saman labbansa yace "Ni ne." "Ah lallai yau nazo a sa'a, Hajiya Babba kinyi babban bako mutanen turai da basa ziyartar yan uwa." "U r not serious!" Yace suna karasowa tsakiyar falon in da second set din kujerun suke kuma in da Hajiya Babban take tana karatun Qurani akan dan katakon ta. "Sannun ku da zuwa." Tace tana rufe karatun ta yunkura da dan k'yar ta mike daga k'asa idon ta akan Jidda dake ta sunne kai cikin taraddadin abinda zata tarar "Bismillah, zauna mana Hauwa'u." Ta kira ainahin sunan nata da Baba ne kawai yake fada mata a yanzu sai ko course mates dinta, nutsuwa taji kad'an ganin a kalla tasan wacece ita har ta kama sunan ta haka radau. Zama tayi a k'asa Tariq kuma ya haye kujerar sai ya dan zamo kadan yace "Hajiya barka da gida." "Ba zan amsa ba." Tace tana kauda kanta, ta dawo kan Jidda tana share shi "Dalilin ki Tariq yazo gidan nan,dan rashin kirki." Sunkuyar da kai Jidda tayi ta danyi dariya kad'an "Ba zaki kulani ba granny?" "Ba dan ni kazo ba, yanzu ace Tariq gidan nan kamar baka san hanya ba,yaushe rabon ka da kazo? Itama uwar taka da laifin ta wallahi." "Ayi hakuri Hajiya kinsan turawa basa san mutane sosai." "Kana da matsala." Yace yana kallon al'amin din "Sai su ci kansu ai." Tace tana daga wayar dake gefe da take communicating da duk ma'aikatan gidan "Nayi Baki." Tace ta katse "Malam ya gida ya aiki? Ya kwana da yawa?" "Alhamdulillah wallahi, aiki ana lallabawa gashi nan ba dadi, kai fa?" "Toh gashi nan dai, zan koma ne ma cikin next week in sha Allah." "Kace zaka sake guduwa sai an kuma ganka kenan." "A ah fa." "Ai naji aikin naku ne kullum kuna tafe shiyasa, ina wani time na irin wannan ziyarar." "In sha Allah ma.zanzo, zan shigo gidanka ma kafin mu bar kano muzo mu gaida madam." "Da ka kyauta kuwa." "In dai Tariq ne ba zuwa zai ba fa, shi in dai harkar mutane ne toh babu shi a ciki sam." "Haba Hajiya ba haka bane ba." "Fadawa wanda be sanka ba." "Hauwa'u, tashi ki zauna sosai kinji?" "Nan ma yayi Hajiya " "Toh bari na shiga ciki na turo miki Nu'ayma, idan kuma zaki shigo cikin ne toh." "Nu'ayman tazo Hajiya." Yayi charaf ya amsa kamar dashi ake. "Ok toh, ka biyo ni inason ganin ka." "Dollars zaki bani ko pound sterling?" "Duk wanda kake so." Dariya sukayi shi da al'amin ta shige ciki, maimakon ya tashi ya bi bayanta sai ya kasa dan ba zai iya barin ta daga ita sai al'amin din me shegen surutun tsiya ba, jira yayi sai ga Nu'ayma ta fito da fara'arta, ta gaishe su sannan yace ta kai Jiddan dakin su. Tashi Jiddan tayi ita kuma ta daukar mata snacks da juice din da aka kawo mata suka shiga ciki, sai sannan ya tashi yabi bayan Hajiya Babba ya bar al'amin din shi kadai! [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**       ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*                   Page (54) ***Sun jima a gidan Hajiya babba fiye da yadda tayi zato ko tsammani, suna daki sai ga aunty Mimi ya shigo cike da murnar ganin Jiddan wadda ita tayi duk kokarin ta wajn wayarwa da Hajiya Babba kai akan Jiddan da yanayin halin kirkin ta, a dah su Nafi sun fanfa ta amma da Anty Mimin ta yi mata bayani sai taji ta sauka sosai, har ma tana son Jiddan shiyasa da tazo tayi mata tarbar da Jiddan batayi tunani ba.   Sun fito zasu tafi bayan an saka mata kyautar Hajiya Babba a booth suna sake yin sallama sai ga Anty Nafi da Salma sun shigo a motar Anty Nafin driver ya kawo su, kallo daya Tariq yayi musu suna shigowa ya dauke kansa ya shiga motar sannan ya zuro kafafuwan sa waje yana zaro wayar sa, maganar da Hajiya babba tayi masa kenan a ciki akan maganar Anty Nafin da abinda ya faru yayi mata bayanin komai shine ta kira tace su zo ita da Salma sai gasu sun iso dan dawowar su kenan ma daga Abujan ko kaya basu chanja ba suka fito dan dama ko hajiyar bata kirata ba tayi niyyar zartowa tazo ta fada mata irin wulakancin da Mama tayi mata akan Tariq. Mamakin ganin Tariq din da Jidda a gidan yasa ta fitowa da dan sauri bayan ko gama parking daidai driver be ba. "Tariq dai kaki barin Jidda da tayi zaman ta anan ai, Hajiya ma zata ji dadi." "Anty zamu dawo, yanz akwai in da zamuje daga nan ne." "Toh shikenan, sai kun dawo din." "Sai anjima Anty Mimi." "Sai anjima Jidda, bye." Baya ta shiga shi kuma dama yana gaba tare da driver sai dayar motar da take bin su, suka fita daga gidan yana kallon mirror din gaba yaga sanda Anty Nafin ta karaso tana kallon motar tasu ita ma yar iskar yarinyar idon ta akan motar. Shafa kansa yayi yana jin wani dum kamar wanda yayi wani babban aiki. Direct gida aka wuce dasu daga nan. Gidan da ma'aikata masu kula da gidan dan yanzu yawanci Baba anan yake weekends kuma mafi yawancin lokuta tare suka zuwa da Mama dan itace me sabgar yi ga shagunan ta dan ma fauwaz shine karfin kula da duk wasu business dinta shiyasa ko yaushe yana tsakanin Kano din da Abuja yana duba yadda abubuwan suke tafiya.   Daga bq ta fito ta bawa Jidda key din part din nasu da aka sake gyara shi dazu, mika masa tayi ya karba yana amsa waya ya bude sannn ya matsa mata ta shiga sannan shima ya shiga yana jan suitcase din su zuwa ciki yana cigaba da wayar sa. Ta rasa gane dalilin sauyawar sa lokaci d'aya, duk da haka suna yawan had'a ido amma sai ya fuske yana cigaba da wayar da take tunanin kamar da gayya yake jan hirar. Kayan nasu ta dauka tayi ciki tana kallon sanda ya bita da kallo. A gefe ta ajiye kayan tana karewa bedroom din kallo me dauke da hadadden royal bed din da aka sakawa red bedsheet me zanen heart. A gefe ta zauna ta fito da charger ta, ta jona wayar ta sannan ta nufi toilet din dake manne a falon. Wanka ta fara yi sannan ta dauro alwala ta fito daure da towel Babba. A wajen kayan su ta ganshi yana duba abu, tayi kamar bata ganshi ba saboda rashin kayan dake jikin ta, kad'an ya kalle ta sai tayi tunanin zai mata magana amma kuma sai ya cigaba da abinda yake kamar shima be ganta ba. Juyawa yayi ya fita, jiki a sanyaye ta shirya ta yi sallah sannan tazo ta dauki wayar ta,ta kira  Safeera dan taga kiran ta sanda suna gidan Hajiya Babba .    Suna cikin wayar ya shigo sanye da  dogon wando fari da t-shirt kamshin turaren sa ya cika dakin daga gani wanka yayi babu ko tantama. A gefen ta ya zauna ya saka hannu ya zare mata wayar daga kunne sannan ya katse kiran yana kallon ta "Haka ake lallaba miji?" Ya kalle ta rike da wayar bayan yaga da wadda suke yin wayar. "Na'am?" Tace a dan kaikaice tana kokarin hana idanun sa tasiri akanta "Eh, haka akeyi? Baki san fushi nayi ba?" "Fushi? Me yasa?" "I'm jealous, kishi nake and you just pretend as if baki gani ba ma." "Kayi hakuri." "Ai kinji... A dake ka a hana ka kuka, ayi maka laifi a yi saurin baka hakuri da kazo zakayi yar mitar ka." "I'm so sorry ba zan kara ba.” “Ni ba zan hakura ba!” “Please…” “Sai da sharadi idan kinaso na hakura.” Kallon shi tayi ya kashe mata ido “Sai kin saka min rigar nan kin yi fashion parade sannan zan hakura.” “Innalillah!” “Yea! Idan ba haka ba nayi ta fushi na daina kulaki!” Ya juyar da kansa gefe daya yana turo baki kamar karamin yaro. “Shikenan zanyi, amma sai dai anjima!” Juyowa yayi yana murmushi “Why not now? Me yasa sai anjima?” “Ni dai kawai.” “Shikenan I will wait! Amma karma kizo min da wani excuse wallahi. Inaso naga matata ehe.” “Tell me, waye wannan ismail din? How much did he know about you?” “Ba zamu kyale maganar ba?” “No it’s better ayi ta kawai Jiddaaaa.” “Ok, yayan Safeera ne, both of them helped me alot a rayuwa ta, sun so ni a yar kauye ta da rama ta, basu taba kushe ni ba ko aibata ni.” “OMG!” Yace yana kokarin rike ta, ta dan matsa kadan tana kin kallon sa “He nuna interest akaina and I said no, be takura min ba, he left daga nan aka daura min aure, and I waited for good 1year, since then ban sake ganin sa ba coz dama a time din ya tafi karatu, this is the first time bayan long time da na ganshi, and yasan nayi aure, kuma nasan babu wani abu a ransa.” “Jiddah!” Ya kira ta ganin yadda mood dinta ya sauya. He misunderstood everything yazo yana ta fushi akan iska. Kin kallon sa tayi saboda yadda idanun ta suka cicciko zatayi kuka. Juyowa da ita yayi suna kallon juna, tayi saurin sauke kanta kasa ya sa hannu ya tallafo fuskar ta. “I’m so sorry kinji? Dan Allah Kiyi hakuri ki daina tuna abinda ya wuce, nayi kuskuren fadan abubuwan chan Amma wallahi wallahi ba har zuciya ta ba, I was just looking for an excuse to hold on to, ba nayi ne don cin fuska ba, dan Allah forgive me! Wallhi nayi regretting, I regret everything har rashin dawowa ta,forgive me dan Allah!” Kuka tasa masa ya jawota jikinsa ya rungume zuciyar sa na wani irin zafi, yasan zata dade bata manta ba, bayan ka zauna zaman jiran mutum ba shekara daya amma ya dawo yace baya son ka, dole da ciwo ontop of that kuma ma ya hada da kushe ka, dama zai iya dawo da lokacin baya ya goge duk abinda yace din, Amma Yanzu kam it’s too late. Ta dan dade tana kukan kafin tayi shiru sai ajiyar zuciya da take a hankali, tana da saurin kuka karamin abu yanzun nan zai sakata kuka sosai, bayan ta yake tapping a hankali ya kasa ce mata komai har tayi shiru din. D’ago ta yayi yana kallon yar fuskar tata, hannun sa yasa ya goge mata ragowar hawayen da take ya shafi saman lips dinta da yake ganin shine kawai last option dinsa da zai yi amfani wajen sake bata hakuri. “I’m sorry.” Yace muryar sa ta shige ciki sosai. Sai ya matso da fuskar sa daf da tata, ya dora hanci sa a saman nata yana gogawa kadan kadan yana kokarin saka mata idonsa a cikin nata saboda taga how sorry he is, a hankali ya kai bakin sa saman nata ya hade su waje daya, sannan ya sa hannun sa ya zagaye ta cikin ta ya matso da ita so so close. Kusan minti biyu ya dauka yana kissing dinta a hankali, kafin ya cikata yana maida kansa ya hade goshin su waje daya, idon ta a rufe yake jikinta yayi wani irin sanyi, ya riga ya gano lagon ta. Kissing aaman “Please Kiyi hakuri, ki daina tunawa kinji? Ya wuce ba zan sake ba. I love you so very much, bansan irin son da nake miki ba wallahi! Kukan ki is one of my weaknesses dan Allah ki daina kinji?” G’id’a mishi kai tayi, ya rike hannun ta yana mata murmushi “Did you love me?” Ya tambaye ta for the first time cike da tsoron kar tace masa a ah. “Umm? Kina son Ya Tariq dinki?” “Eh…” ta daga kanta kunya na cikata “Yes! Say it naji, pleaseee.” Kasawa tayi, ta boye kanta a kirjin sa tana dariya kadan kadan “Kunya kike ji?” “Umm…” “Ni dai sai kin fada min naji.” “Ba zan iya ba.” “Zaki iya, pleaseeee!” Yawun bakinta ta tattaro fuskar ta har lokacin na cikin kirjin sa, “Na rufe ido na, inajinki fada mjn, tell me you love me.” Dagawa tayi kadan taga ya kulle idon sa, kallon fuskar ta dinga yi tana admiring din ta, ta dan kai hannu kadan ta taba gefen sajen sa, ya rike hannun yayi kissing dinsu still idon sa na a rufe “I’m waiting…” “I love you so much.” Tace da sauri kamar wadda aka tunkuda. Dariya ta bashi amma sai ya kanne ya bude idon sa “Wow! I love you more baby.” Yace yana mata murmushi [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__** ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*               Page (55) ***Kallon hanya take cike da murna da farin cikin zata ga Baffan ta, yana lura da yadda ta cika da doki yayi murmushi yana murza hannun ta kad'an da yake cikin nashi tun sanda suka soma tafiya. Suna baya a zaune sai driver a gaba da mutum daya. "Bafa kwana zakiyi ba." Yace ta juyo da sauri tana kallon sa "Yes!" Ya dage mata gira "Na dade ban zo ba fa." "Zaki dawo ne, banda yanzu amma." "Dan Allah." "Nah!" "Dan Allah Dan Allah!" "Um um naki, tare zamu koma. Nayi missing dinki." "Missing?" "Ehen, ba zan iya hakuri ba jiya dai kin yi min wayo amma banda yau." "Please dan Allahhhhh." Taja muryar ta cike da shagwaba "La la la la,na murza gashin baki." "Pl...." Hannu ya dora mata akan lips din nata yana girgiza mata kai "Don't beg me pls, or i will kiss you." Hadiye maganar tayi tana yin raurau da ido, yayi kamar be gani ba ya juyar da kansa yana murmushi. Bata sake magana ba har suka isa cikin garin ta soma ganin mutane kad'an kad'an har suka karasa kofar gidan nasu da ya samu sauyi sosai fiye da yadda tazo ta ganshi a baya. Baffan ta, ta hango yana tahowa daga hanyar kasuwa sanye da shadda fara tas daga gani sabuwa ce hannun sa rike da leda baka fuskar sa dauke da murmushi wanda ya kasance sunna. "Baffa." Ta motsa bakin ta a hankali tana murmushi, kallon wajen yayi ya kurawa baffan ido, kasancewar ya jima be ganshi ba tun wani zuwa wajen Baba da ya taba yi sai yaga ya sauya masa sosai, kamannin sa da nutsuwar sa sak na Jiddan sa,hatta da tafiyar ta irin tasa ce. Bud'e motar yayi da dan sauri ya fito ya nufi wajen baffan tun kafin ya kai ga karasowa ya durkusa har k'asa, sai a lokacin baffan ya lura da su dukka ma, ya fadada fara'ar fuskar sa zuwa ta musamman "Baffa barka da warhaka." "Barka dai d'ana, zuwan kenan? Sannun ku da zuwa." "Zuwan kenan," ya mika hannun sa ya karbi ledar hannun Baffan, ya sakar masa yana jin dadi idon sa akan Jidda dake tsaye tana murmushi. "Muje ciki kaji, sannun ku da zuwa maraba." Mikewa yayi yabi bayan Baffan yana kallon idanun Jiddan da suka kawo ruwa kamar zatayi kuka, yadda yayi wa baffan yafi komai yi mata dadi, a kalla ya girmama mahaifin ta girmama mafi girman gaske. "Baffa." Tace tana matsawa kusa dashi ya yi yar dariya yana cewa "Kin ganki ko? Ba dai kuka zaki mana ba." "Ka ganta nan bata girma Sam, duk sanda tazo sai tayi kuka saboda shirme." "Murnar ganin ku ce Baffa." "Kai dai kare ta kake." Yace sanda suka shiga zauren gidan, kallon ta yayi ya girgiza mata kai a hankali k'asa kasa yace "Don't waste my tears please." Ta jishi sai kawai ta shige ciki da sauri ta bar su suna kokarin shigowa tunda Baffan a hankali yake tafiya ssosai duk da kafar sa ta samu sauki amma kuma yana dan lallabawa. Iya Lami na zaune a kofar dakin ta da yasha fenti da duk dakunan da suke cikin tsakar gidan nasu in da taga sabon gini daga gefen dakin baffan, kafin ta gama tunanin yaushe akayi hakan sai ga wata mata farar dattijuwa ta fito tana duba abu a kofar dakin kafin dukka su lura da Jiddan da take kallon gidan nasu. "Jidda!" Iya Lami tace tana mikewa rike da gefen zanin ta ta hau gyara shi tana washe baki. "Jiddan Bingel? Ah maraba lale da mutanen birnin taraiya " Matar tace tana sakin murfin kofin da ta dauka a hannun ta tayo wajen Jiddan tana wuce Iya Lami da ta saki baki ta dakata da karasowa. Murmushi me kama da yake Jidda tayi ta gaida matar wadda ta cika da murnar ganin ta tamkar ta santa ko ta taba ganin ta. "Sannu da hanya Hauwa'u, sannu da zuwa wuce muje ciki." "Malama ki kyale yarinya da gidan ubanta ai tasan gidan ba sai kin nuna iyayi da kinibibi ba, uwar munafukan duniya." "Shigo nan Jidda." Tayi banza da maganganu Iya Lami din ta kama hannun Jiddah zuwa dakin da tafito, tayi saurin shinfid'a mata tabarma sannan ta debo ruwa me sanyi a randar ta dake gefen dakin ta, ta kawo wa Jiddan hade da mahuci saboda yanayin zafin da ake a garin da ya dan busa wanda ake kira da daure cikin dawa. Zama tayi a kubin Jiddan ta dauki muhucin ta hau mata firgita sai ga Baffa ya shigo Tariq na biye dashi har cikin dakin da Jiddan take ba tare da ya kalli ko da bangaren da Iya Lamin ke tsaye ba. Wata tabarmar ta mike ta sake shinfidawa kafin taja mayafi ta rufe kanta ruf sannan ta zauna tana amsa gaisuwar Tariq din. "Yau dai ga yarki nan na tazo tare da Maigidan ta, shikenan sai murna." Yace yana dariya "Aikuwa yau ina cike da farin ciki mara misaltuwa, buri na kuwa ya gama cika." "Baffa na ina wuni?" Jidda tace tana shagwabe fuska ganin kamar yafi damuwa da ganin Tariq din a kanta "Lafiya Lou, alhamdulillah sannun ku da hanya." "Baffa! Bakayi murna da gani na ba?" "Nayi murna mana Jiddan Anty." Yace cikin sigar zolaya, "Sai dai nafi murnar ganin dana Tariq." Murmushi Tariq din yayi suka hada ido da Jidda ya kashe mata ido daya ta turo baki gaba tana kin sake kallon sa. Dago labulen akayi Iya Lami ta shigo ta samu gefen kofar dakin ta zauna "Maraba sannun ku da zuwa." "Yawwa." Tariq ya amsa jidda kuma ta amsa a ciki tana kin bata wani attention dan ba zata taba mantawa da Iya Lami a rayuwar ta ba, ta kuma kasa manta memory din wahalar da tasha a wajen matar. Shiru ne ya biyo baya dan shi kansa Baffa ba wata doguwar magana ce take hada Shi da ita ba shiyasa ma daga karshe yayi auren sa ya auri kawar Maman Jiddan da Mijinta ya mutu sai dai bata taba haihuwa ba, tun daga lokacin rayuwar Baffa ta chanja ya murmure ya dawo cikin nutsuwar sa ya bar Iya Lami da bakin halin ta wanda ko a yanzu tayi nadama dan dai kawai baya son ya sakata a cikin irin masifar da ta sakashi shida Jidda amma da sakin ta ma kawai zai yi ya huta, amma ko  a hakan ma ya barta ya isheta dan shi kam idan ka cire hakkin aure da yake kanshi babu wani kuma da zata nema a wajen sa. Fita waje tariq sukayi shi da Baffa suka barsu a ciki,Inna suwaiba da ta riga ta gano matar Baffan ce ta shiga nan nan da ita tana tarairayar ta kamar kwai, nan da nan ta hau girki bayan ta tambayi Jiddan abinda take so tace mata dambu. Nan da nan ta tashi aikin sa ita kuma Jiddan ta fada gidan su Saude ta samu Innar su tana wanki aikuwa tayi murnar ganin Jiddan ta tsame hannu ta zo suka zauna hirar yaushe gamo tana yi tana zuzuta Jiddan da yadda ta zama tamkar balarabiya saboda yadda ta sake fari da wani irin kyau na ban mamaki. Ta dade a gidan har sai da Inna suwaiba ta aiko tazo taci abinci sannan ta dawo tana shigowa bata dade ba Innar su Saude ta aiko mata da danwake. Taci dukka sosai ta ajiye ragowar na anjima haka aka kaiwa su ma wanda suka zo tare waj da ruwa da Baffa ya samo musu na pure water sannan ya samo fura me kyau aka damawa Tariq din da fresh madara me dumi. Sosai ya saki jikin sa musamman da yaga baffan na ta kokarin sai ya sake dashi dan hatta abincin tare suka ci sukayi sallah ya kuma rakashi daya daga cikin shagon sa na kasuwa ya gani sannan ya nunawa jama'ar sa shi a matsayin Mijin Hauwa'u.   La'asar likis yayi mata text yace tafito su tafi, kwalla ta ciko mata tayi masa reply da dan Allah ya barta, ko sakan batayi da reply din ba sai gashi sun shigo ciki shi da Baffa, kallon ta yayi ta marairace masa ya kauda kansa yana amsa maganar Baffa da yake masa "Tashi maza ki shirya kar dare yayi muku, ashe wai sallamar abokan tafiyar taku kayi sai da muka dawo naga basa nan." "Eh wallahi, naga kaamar zasu gaji ne kuma dai dama ni ba wani so nake ba Baffa " "Toh sai ku hanzarta ku tafi Allah ya tsare, Allah ya kiyaye ya bada sa'ar tafiyar da za'a yi ya kuma bada abinda za'a je nema." "Amin Baffa." Yace yana dan dukawa. Tashi tayi ta shiga ciki ta dauko handbag dinta da mayafi tana share kwallar da take kokarin zubo mata saboda yadda taso kwana tayi hira da Baffan ta gashi ba nan kusa zata dawo ba, ya kasa fuskantar yanayin ta, kansa kawai ya sani sai taji kamar be kyauta mata ba. Fitowa tayi tana kin kallon shashen sa, ta russuna tayi wa Baffa gaisuwa muryar ta na rawa sannan tayi wa Inna suwaiba da Iya Lami da ta zama yar kallo. Tausayin ta ne ya kama Baffa amma ya basar yana sake cewa suyi maza su tafi kar su yi dare, amma ya lura da yanayin Jiddan shima kuma zai so ace ta kwanan tunda kasar zasu bari gabaki daya amma ya zai yi? Tunda ya lura Tariq din be amince ba. Yana gaba tana bin shi a baya har wajen motar da ke cike da yara sunzo kallo, da kansa ya bud'e mata yana saka idon sa a nata amma taki yarda ta kalle shi, sai da ya rufe mata kofar bayan ya gyara mata veil dinta da ya fito sannan ya sake sallama da Baffa dake tsaye Inna Suwaiba na daga bayan sa ta cikin zauren sannan ya shiga motar ya tada suna daga musu hannu ganin an fara tafiya kawai sai ta fashe masa da kuka sosai. *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__** ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*               Page (56) *** Tafiya yake yana kallon gaban sa yana jin yadda kukan ta yake shigar masa ilahirin dukkannin jikin sa, baya so ya tsani duk wani abu da zai sakata kuka gashi ita abin kukan baya mata kad'an kwata-kwata. Birki ya taka ta dago ya zuba mata ido bayan ya saka motar a parking. "Bakya so ki bini?" Shiru tayi tana kokarin daidaita kukan nata "Shikenan, zan maida ke sai na tafi, idan kin gama sai nazo mu tafi, hakan yayi miki?" Girgiza kai tayi "Mu tafi." Tace cikin muryar kuka "No bakya so, kuma be kamata nayi forcing dinki ba, kina so kuyi magana da Baffa ko? Kinyi missing dinshi ko?" Daga mishi kai tayi "Shikenan ki daina kuka, I'm taking you back, sai na dawo mu tafi." "Um um mu tafi kawai dare zai maka idan ka koma." "Sai nima na kwana." Yace yana kallon ta "Sai ka kwana." Tace tana murmushi "Wasa nake miki, ina ni ina kwana gidan surukai? Sai dai idan tare zamu kwana." Boye fuskar ta, tayi a cikin mayafin ta, yayi murmushi sannan ya shafi gefen fuskar ta, ya cire motar daga P ya maida ta R ya juya kan motar zuwa hanyar da suka biyo.    Ido Baffa ya kura yana tunanin da gaske ne ko dai gizo idon ke masa, sai da suka matso sosai ya tabbatar da su ne suka dawo, ajiye butar hannun sa yayi yana jiran Tariq din yayi parking sannan suka fito. "Lafiya?" Baffan ya tare su tun ma kafin su karaso, kasa Jidda tayi da kanta shi kuma Tariq yayi murmushi "Lafiya Lou Baffa, dawo da ita nayi ta kwana." "Akan wanne dalilin? Wato uzzura maka tayi ka dawo da ita kenan saboda bata da kirki ko?" Da sauri yace "A ah Baffa, ni dai naga dacewar hakan, tunda idan mun tafi zamu iya jimawa kafin muzo." "Ban yarda ba, ba wani ita ta saka dole ka dawo da ita, maza ku juya kibi mijinki bana son shashanci da sakarci." Ya cigaba da fada sosai irin wanda Jiddan bata taba ganin yayi ba, kanta a k'asa tana hawaye ta juya kamar munafuka tayi hanyar motar daidai lokacin da aka soma kiran sallar magriba a masallacin kusa dasu "Baffa dan Allah kayi hakuri ka barta dan Allah." Tariq din yace yana rokon Baffan "Sai dai kaima toh ka zauna gobe da safe sai ka tafi, amma sam ba zaka bi hanyar nan kai daya ba ga dare, kuma ko gaba ba'a biye wa shiriritar mata dan su ba ishashen hankali suke dashi ba, zo ki shige ciki kuma zamu hadu dake idan mukayi sallah." Juyowa tayi sum-sum-sum ta shige shi kuma ya mikawa Tariq din ruwa a buta yace yayi alwala sannan suka nufi masallaci. Tana kan abun sallah tana tunanin rashin kyautawar da tayi sai ga sallamar Baffa, sai kuma ta Ya Tariq din da yake biye dashi. Rufe kanta tayi da Hijab din da tayi sallar cike da tsoron haduwa da Baffan. "A gyara wanchan dakin ga net nan sai a saka masa a rufo dakin ." "Toh Malam." Tace cike da girmawa "Baffa da an barshi ma na gyara da kaina." "A ah ba za'a barka ba, bismillah zauna." Zama yayi sannan Baffan ya zauna shima yana kallon kofar dakin da yasan Jiddan na ciki. "Hauwa'u." "Na'am." Tace ta fito da sauri "Jeki taya Mamaanki ku gyarawa megidanki dakin chan." "Toh." Tace ta wuce a tunanin ta ko wani fadan zai mata da taji kiran. Zuwa tayi ta samu Inna Suwaiba a dakin ta tayata suka gyara shi tsaf, dama akwai yar katifa madaidaci a dakin da carpet yawanci anan Baffa yake kwana ko idan yayi baki ya shigar dasu ciki sai toilet dan karami da banbun ruwa da already yake cike da ruwa. Babu wani datti a dakin nan da nan ta gyara shi ta gyara shinfidar gadon ta samu gefen katifar ta zauna tana tsoron fita su sake haduwa da Baffa yayi mata fada. Tana zaune tana dan jiyo maganganun Baffan da nasa kafin taji sanda Baffan yace masa zai je baya ya dawo ya shiga ciki sauro. Dama yana lura bata fito ba tunda ta shiga, rabin hankalin sa yana chan shiyasa baffan na cewa ya tashi ya mike yana yi masa sai da safe har Baffan na tsokanar sa ba zai dawo su cigaba da hirar ba, murmushi kawai yayi Baffan ya fice shi kuma ya nufi dakin da dan saurin sa. Tana jin fitar Baffan ta yinkuro zata fito kafin ya dawo ta kwanta sai gashi ya turo kofar ya shigo. "Ina zaki?" Yace yana tokare kofar da hannun sa "Daki zan je kafin Baffa ya dawo, kar yayi min fada." "Ba zai sake miki ba ai." "Um um baka san Baffa ba, zai iya sakewa wallahi." "Ba wani, ai ya wuce na masa bayani ni nace mu dawo ba bake ba " "Ni ai tunda Baffa ya ganka ya daina so na." "Shine kike kishi dani?" "Eh." Ta daga kanta "Yarinya haka zaki hakura, na riga nayi miki fashin Baffa kamar yadda kika kwace min Baba." "Ni din?" "Ehen, Baba yana son ki komai Hauwa'u komai " "Nima inason Baba sosai." "Shikenan an raba, ke Baba ni Baffa." "Ni dai dukkan su nake so." "Ai baki isa ba sai dai ki zabi daya." "Um um dukka nake so ni dai." "Idan kinaso na bar miki su sai dai ki kwana a dakin nan." "Innalillahi!" Tace tana waro ido "Sai da safe " tayi hanyar fita da sauri tuno waye Tariq din, hannun sa da ya tokare kofar ya sake gyarawa sosai, tazo ta sa hannun ta wai zata cire hannun sa, dariya ma ta bashi ya tsaya yana kallon yadda take cijewa a dole sai ta cire hannun sa, sai da ta gama duk kokarin ta ko gezau bayayi sannan ya cire hannu ya fizgo ta gaba daya jikinsa ya matse ta yana dora habbar sa a saman kanta "Karfin ki be fi cikin tsokali ba kece zaki iya cire hannu na Baby?" "Ai dan na hakura ne." Tace "Auw, haka kika ce?" Ya cireta daga jikin nasa yana kallon fuskar ta, daga masa kai tayi alamar eh "Ok bari mu gwada wani abu " Sai kawai ya dagata sama baki daya nufi katifar da ita, da sauri ta hau wuntsila kafarta ta hau rokon sa "Dan Allah kayi hakuri." "Abu zan gwada kawai, muga karfin da kike dashi." Sauke ta yayi kafin ta yunkura ya bi ta ya dora mata dukkan nauyin sa akanta, yayi mata rumfa da jikinsa har baka iya ganin ta. "Oya show me your strength." Girgiza masa kai ta hau yi "Ba zan kara ba, pls ka dagani wayyo Baffa na." Toshe mata baki yayi da sauri yana mata dariya, sai da yaga ta fara jigata sannan ya dagata kadan ya juyar da ita ta dawo saman jikin sa suna kallon juna. "I love you Jiddanah." Ya samu kansa da furtawa cikin wani irin shauki. "Bayan ka danne ni." "Wasan soyayya ne, kuma kinga ai gwara ki saba daukata, kin gane?" "Ni ba ruwana." Tace tana juyar da fuskar ta da sauri "Shy shy girl." Ya danna mata hanci yana murmushi "Zan tafi, kafin Baffa ya dawo." "Ni gaskiya a'ah, gaskiya!" "Ba zan tafi ba?" "Eh." Ya daga mata kai "I need my wife a kusa dani gaskiya." "Ni dai dan Allah kayi hakuri, kar Baffa ya shigo." "Ba zai shigo ba ai." "Allah zai iya dawowa yazo, dan Allah ka barni na tafi." "Zaki dawo toh?" "When?" "Idan Baffa yayi bacci, kowa yayi bacci." "Um um ba ruwana." "Toh ba in da zaki." Ya hau goga fuskar sa a saman tata, kafin ya ciji lips dinta na k'asa a hankali, shi kadai yasan me yake ji a game da ita, wani irin magnet ne yake jan sa, she's sooo sooo sweet da baya iya resisting kansa, yanzu ma kawai dan babu yadda zai ne amma he's desperate to be with her, motsin shigowar Baffa yasa shi daga ta ba dan yaso ba, ta fice da mugun sauri. Fadawa yayi saman katifar ya rike kansa kad'an sai kuma ya mike ya fito domin dauko abu a cikin motar sa. Tsire Baffa ya siyo masa da lemuka ashe shine fitar da yayi, ya kawo masa har bakin dakin be shiga ciki ba ya fito ya karba yayi godiya sosai dan be so Baffan ya wahalar dashi haka ba. Jidda yasa aka kira masa suka zauna a waje daga kofar dakin sa suka shiga hira, hira irin ta tsakanin d'a da mahaifi, dama chan yana so ta kwanan dan dai ba zai nuna bane, yaji dadi matuka yadda Tariq din yake kular masa da Jidda kuma hankalin sa ya kwanta sosai. Sai wajajen sha biyu sannan Baffan yace taje ta kwanta ya shige dakin sa. Tana shiga daki yana kiran ta a waya, tayi kamar ba zata daga ba dan har ta soma cire kayan jikin ta ta daura zanin Inna Suwaiba da ta fito mata dashi, mayafi ta yafa akan zani da rigar ta fita a hankali cikin sand'a ta isa tana zuwa yana jikin kofar ya riko ta da sauri ciki ya maida kofar ya rufe yana sauke ajiyar zuciya "Na zata ba zaki zo ba." "I missed you." Yace yana zagaye fuskar ta da tashi. "Gani." "Ok muje mu kwata!" Yaja hannun ta "Aina?" "Anan mana, plsss don't say no, bansan me yasa ba nake jin wani irin feeling, dan Allah karki tafi ki barni." "Idan Baffa ya fito fa." "Ba zai fito ba, sai ki koma kafin asubah kinji Jidda nah." "Ni dai..." "Shsshh, babu kyau fa, mala'iku zasu tsine miki, don't say no again kinji?" Shiru tayi tana kallo ya cire mata mayafin ya ajiye a hankali sannan ya jata zuwa jikin sa ya sauke ajiyar zuciya da karfi wanda har sai da taji tsoro. *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________*     *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_  350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 *(Mss xoxo)* 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350    *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350     *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350      *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350     *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350     *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 1k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_  *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__** ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*               Page (57) ***Rawar sanyi take tun da ta fito daga toilet din, zanin gadon ya cire da sauri ya rufa mata yana rungume ta jikinsa, ji yake tamkar ya sauke wani gungumemen dutse daka akan sa da yake a chunkushe sosai, baya jin wani rashin kyautawa ko rashin dacewar abinda ya aikata din tunda dai ai ba haramun yayi ba, kawai dai ita Jiddan ce take ganin haka amma ya zai yi? Ba zata gane yanayin da ya samu kansa a ciki ba, yadda ya zama so desperate sai yake jin tamkar wani abu ne yake shirin faruwa dashi idan har be aikata ba, amma a yanzu da ya sauke nauyin sai yake jin shi wasai. Ajiyar zuciya ya sauke yana addu'aar Allah yasa wannan tarayyar tasu ta samar masa sanyin idaniyar sa, yana matukar son yara duk da miskilancin sa, be san halin da zai shiga ba idan aka ce masa yau gashi ya zama Baba, musamman ace ya samu cute little baby girl me kama da Jiddan sa, shikenan yasan shi kuma.   A hankali sanyin ya fara raguwa dan dama duk sanda ta zubawa kanta ruwa in dai ba na zafi bane sai ta samu irin wannan matsalar shiyasa ko wanke gashin kanta zatayi sai da ruwan heater take yi. Dago ta yayi yana jawo wayar sa dake kunne ya rage hasken flashlight din sosai ya taimaka mata ta maida kayan jikinta ta sake kunshewa ta tura kanta jikin sa. Kwanciya yayi akan bayan sa ya dora ta a saman chest din sa a hankali a hankali bacci ya soma daukar ta, gyara mata kwanciyar yayi sosai yadda zataji dadi.   Wajen ukun na dare ya farka ya zare jikin sa a hankali ya wuce toilet ya dauro alwala yana fitowa ya sameta a zaune tana murza idon ta, sakko da kafarta tayi ya karaso yana kallon ta "Tafiya zan."     Tace tana jan mayafin ta, hannun ta ya kama ya mikar da ita sannan ya taimaka mata suka fito. Sai da ta shige sannan ya dawo ciki ya shinfid'a abin sallah ya tayar.   Tare suka fita masallaci, achan suka zauna har gari yayi haske sosai kafin su dawo gidan yana zuwa ya tarar da kayan tea da bread sai kosai a plate an kawo amsa hade da farfesun naman zabo. Be so ya tada Baffan a tsaye ba dan yasan saboda shi yake ta hidimar da kashe kudi. Zama yayi yaci sosai kuma yaji dadin farfesun dan shi yafi ci sosai yasha ruwan Lipton. Turo kofar akayi da sallama tana rike da ruwan zafi a dan madaidacin bucket din plastic karami, ruwan wanka ta kawo masa dan ita tayi nata tun dazu har ta saka kayanta. Karbar ruwan yayi a hannun ta yana jin dadin ganin ta, yaje ya juye sannan ya dawo yace ta zauna tayi breakfast din kafin ya fito, toh tace masa ba dan zata zauna din ba dan ta lura shi sam be gane yadda rayuwar take su a wajen su ba. Yana shiga toilet din ta fice haka ya fito yaga ta gudu yayi murmushi kawai ya shirya yana gamawa Baffa yazo yace su shiga ciki ya gaisa da matan gida. Bayan ya shiga sun gaisa sai yace ta fito su tafi dan akwai abinda yake so yayi a kanon kafin su koma da daddare. Fita yayi waje tare da Baffa ya saka aka dauko manyan ledoji niki-niki aka saka musu a booth yana ta cewa a barshi amma Baffa yace ba za'a barshi ba akwai sakon Baba a ciki ma, dama jiya ya nema amma be samu ba da suka dawo shine ya sake aikawa. Godiya sosai Tariq din yayi cike da yabawa dattakon Baffan.   Fitowa tayi zuciyar ta wasai ba kamar jiya ba, ta shiga motar sannan yazo ya shiga suka sake sallama da Baffa sannan suka tafi. Yar tafiya kad'an sukayi Baffa ya kira ta a waya yace su dawo Tariq yayi mantuwa a dakin, envelope ce a ajiye a saman katifar. Katse wayar tayi tana kallon sa "Kayi mantuwa inji Baffa." "Mantuwa?" "Eh wai envelope akan katifa." "Ohh! na Baffa ne ai." "Envelope din?" "Umm." Ya daga mata kai, kiran Baffa ne ya sake shigowa, ta daga yace sun juyo kowa? "Baffa wai yace naka ne." Tace tana kallon sa "Nawa?" "Eh Baffa." "Ina zuwa." Yace yana sake katse kiran ya bud'e envelope din sai ga kudi sababbi kal yan dubu dubu. "Subhallahi."  Da sauri ya kira Jidda tana dagawa yace "Akan me yaron nan zai min haka? Wannan kudin na menene?" "Baffa bansan na menene ba." "Bani shi a waya." Cirewa tayi daga kunnen ta, ta mika masa ya karba yana chanja hannun da ya rike kan motar "Wannan kudin me yawa na menene Tariq?" "Baffa naka ne, a siya kayan abinci bamu zo muku da komai ba." "A ah gaskiya baka kyauta min ba, shikenan kuma sai ka bani kudi masu yawa haka?" "Ayi hakuri Baffa." "Kash! Amma... Toh shikenan Allah yayi muku albarka ya saka da Alkhairi nagode nagode." "Ba komai Baffa." Yayi saurin zare wayar dan godiyar tayi yawa, mika mata yayi yana maida hankalin sa kan tukin ita kuma ta saka a kunnenta tana satar kallon sa "Kiyi min godiya kinji? Allah yayi muku albarka ya kiyaye hanya." "Amin Baffa." Tace a sanyaye sannan ta cire wayar tana dorata akan cinyar ta "Angode Allah ya saka da Alkhairi." Tace a sanyaye, dan waigowa yayi k'adan yayi mata murmushi ya sake maida kansa gaba. Be tsaya ba har sai da suka isa, suka fito zuwa cikin gidan ya shiga ya dauki wasu kayan ya chanja a dan gurguje sannan yace yana itama ta chanja tazo su fita, da sauri sauri ta shirya cikin doguwar riga suka fice daga gidan. A hanya suna tafiya yace mata ina ne gidan su Safeera, kallon sa tayi ya gid'a mata kai "Kirata kice zaki zo, idan na gama sai na biyo mu wuce." Dadi ne ya kamata tayi saurin ciro waya ta kirata tace gata nan. Har cikin compound din gidan suka shiga sai ga Safeeran ta fito da saurin ta, ta tare ta suka gaisa da Tariq din yace zai je ya dawo, suka shiga ciki shi kuma ya fice daga gidan. "Na zata fa da wasa kike da kika ce zaki zo gaki nan." Tace suna haurawa saman balcony "Nima bansan zan zo ba, dawowar mu kenan fa, yace na shirya ashe nan zai kawo ni." "Wallahi ya kyauta, sosai sosai. Kamar yasa nayi missing din best friend dita gashi akwai gist da yawa." "Toh ai gani." "In sha Allah wuni sur zakiyi, musha hira." "Amin, ina Mom naji gidan shiru." "Ai haka kullum gidan namu yake kema kin sani." "Ku ai yan gayu ne shiyasa." "Ba wani nan, Mom tana sama tare da Daddy Ya Isma'il kuwa tun safen wuri ya fice bank sai ni kadai da house helps din gidan, nima dai na kusa dagawa na shige daga ciki na huta da zaman kadaita." "Ah lallai." "Allah kuwa, muje daki kawai idan Mom ta fito kin je ki gaishe ta, yanzu sai ta kai azahar ma bata fito ba " "Allah sarki Mom." Tace suka karasa dakin Safeeran da aka sake gyara shi da kawata shi. Saman gadon ta haye tana cire veil din sannan ta ware gashin kanta da bata iya taje shi ba tun jiya da ta saka masa ruwa. Fita Safeera tayi ita kuma ta mike zuwa gaban mirror dinta. Drawer ta bud'e tana neman hand dryer bata ganta ba, sai da Safeera ta dawo daga kitchen bayan ta jero mata kayan ci akan tray sannan ta dauko mata hand dryer din ta taimaka mata ta gyara mata kan sosai sannan suka zauna zaman hira har Mom ta sauko taje ta gaishe ta sannan suka dawo suka dora ta bata labarin wanda zata aura Sadiq dan har an kawo kudi ma rana kawai zaa saka, tayi mata murna sosai kuma taji ba dadi dan tasan ba lallai ta samu zuwa bikin ba.   Har la'asar sannan Tariq ya dawo yace ta fito, kamar kar su rabu haka dai babu yadda suka so taje tayi ma Mom sallama ta ba wa Safeera kudi ta bata da kyar ta karba suka fito sai ga Ya Isma'il ya shigo gidan a motar sa, da sauri yayi parking ganin wanda yake tsaye a jikin mota a harabar gidan nasu ya fito da sauri ya nufi wajen Tariq din ya mika masa hannu suka gaisa sai yaga ya amsa masa a sake ba kamar jiya ba. "Dama Yayan mu wata magana ce dani." Yace yana dan shafa kansa, murmushi Tariq din yayi yace "Ina jinka." "Dama neman alfarma zanyi, a shige min gaba wajen neman auren Maryam." "Maryam?" "Eh sister din Jidda ba,we met on social media har muka zama friends daga nan ne kuma muka zama lovers, yanzu haka har mun yi magana zan zo naga Baba, idan an amince min." Ya dan dukar da kansa irin respect din nan "Masha Allah, congratulations. Kazo in sha Allah babu matsala." "Nagode babban Yaya, nagode." "Haba ba komai." Yace idon sa na kan Jidda da suka tsaya daga baya ganin suna magana "Baby mu tafi ko?" Murmushi sukayi ma juna ita da Safeera ta kwaikwayi babyn da yace tana mata dariya. Ya Isma'il ne ya bud'e mata motar bayan sun gaisa, ya kara mikawa Ya Tariq hannu suka sake musabiha sannan suka matsa gefe shi da Safeera suna kallon motar tasu ta fice daga gidan. "Rayuwa kenan." Ya Isma'il yace yana murmushi "I'm happy for Jiddah, he's such a nice and cool guy, kuma yana son ta sosai sosai, irin mijin da ya dace da Jidda." "Haka ne, sun dace da juna." "Sun dace kam." "Muje jiki kiji wani labari yarinya, I will soon be getting married." "Are you serious!?" "Allah kuwa,gidan su Jidda kuma zan fada." "Amira?!!" Ta zaro ido "Maryam." "Wow! Dan Allah Yah?" "Allah,maganar da muke dashi Kenan." "Gaskiya naji dadi sosai wallahi, bata da issue ko kad'an wallahi." "I know! Zo muje mu samu Mom, bana so a bata lokaci ban shige daga ciki ba." Dariya suka kwashe a tare suka juya zuwa ciki, ta bud'e murya tana kiran Mom. ***Wajen cin abinci suka wuce sukayi order Chicken Mandi Rice da salad suka wuce gida. Shi kadai yaci dan ita cikin ta a cike yake daga gidan su Safeera. Bayan sallar magriba suka bar gida zuwa airport duk da sai da suka biya wani waje ya karbi sako. Suna shiga Abuja direct gidan su suka wuce dan sai after 10 suka shigo garin ma saboda delay din da aka samu kafin jirgin ya tashi. #Ranooooo ***❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO KISHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__** ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*               Page (58) ***Tun da suka dawo Tariq ya daina zama saboda shirye-shiryen tafiya dan a cikin satin zasu tafi saura be fi kwana uku ba, gashi da shirin tafiyar sa shi kadai yayi da intention din idan yaje zai zo da wuri amma yanzu yasan idan suka shilla suka tafi shikenan kuma sai dai idan haihuwa Jiddan zatayi su zo gida duk da be riga yasan yanayin commitment din da zai shiga achan din ba amma yasan aikin su yana cin time sosai. Maryam da Amira sun zo gidan sau biyu suna wuni duk sanda suka zo tare da sakon gaisuwar Mama suke zuwa duk da jin su kawai take amma kuma hakan na mata dadi matuka, bata san halin da ake ciki tsakanin Baba da Maman ba dan yayi fushi sosai akan Maman shine take neman hanyar da zata samu ya sakko kuma a kasan ranta tana jin nutsuwa idan ta tuna Jiddan ce matar Tariq dinta ba irin Salma ba. Akan case dinta dasu Anty Nafin sai da taje Kano tayi mata tatas hakan ya jawo suka dauke kafa ma daga zuwa gidan Hajiya Babban gaba daya dan sosai Anty Nafin ta kullaci abinda Maman tayi mata. Ana gobe zasu tafi Anty tazo ita da Usman, kamar Jidda ta zuba ruwa a k'asa tasha saboda murnar ganin Antyn. Dama lokacin tana karasa hada kayan ta waje daya ne sai ga Antyn aikuwa ta tayata suka karasa tare suna aikin tana shigar da sakon da take son nunawa Jiddan cikin hikima da yadda zata kula da mijin ta, ta sake samun fada a wajen sa. Jiddan naji duk tana daukewa dan dama Antyn ce mirror dinta ita take dubawa a abubuwa da yawa saboda tasan babu abinda ya zaunar da Antyn a gidan har ta kawo yanzu sai hakuri da iya zama amma ba dan haka ba da tuni ba wannan labarin ake ba. Ya Tariq ne ya kirata bayan yaji komai lafiya sai take fada masa Antyn tazo shineyace kawai ta bita su tafi tare idan ta tashi tafiya saboda su yiwa Baba, Yaya da Mama sallama dan fitar asubah zasuyi gobe daga nan shima idan ya gama gidan zai wuce sai su dawo tare. Toh tace ta ajiye wayar ta fadawa Antyn abinda yace. "Hakan yayi." Tace. "Tunda tare zamu tafi ai sai mu hau shiri, komai ya riga ya shiga jaka sannan wadannan abubuwan da na nuna miki su karki wasa dasu wallahi." "In sha Allah ba zan ba Anty." "Yawwa, Allah dai ya kaiku lafiya, idan mun koma kika je part din Maman Fauwaz ki zauna sosai kinji? Karki ce zaki taso daga zuwa." "Sau biyu da su amira suka zo sai suce wai Mama tana gaishe ni." "Kai haba? Da gaske ko wasa?" "Allah haka suka ce, na karshen ma Amira tace wai Mama tace mu fadi me muke bukata na tafiyar, shine sai yace tace mata zai zo gidan dan dama yana nan." "Toh Allah yasa addu'ar mu ce taci ta, hakan ai kinga yafi, a kalla zamu fi samun kwanciyar hankali, kuma kinsan Allah? Maman Fauwaz bata da damuwa ita dai barta da kishi da duk mace kuma tana dashi sai dai kowa da irin yadda yake bayyana nasa, amma ko bayan wannan ba ruwanta da rayuwar ka, ko a sanda nake mata aiki bata da irin takurar nan magana ma bata cika son yi ba shiyasa ake mata kallon mara kirki, amma kishi ne kawai ya sakata yin duk abinda take amma sam babu cutarwa." "Haka ne gaskiya." "Allah ya kyauta yasa sakkowar tata kenan tunda dai yanzu ta zame miki dole tunda kika auri dan ta, ba'a kuma san karshen zaman da kuma yayan da za'a haifa ba." "Ni ba zan haihu ba Anty." "Saboda me?" Tace da sauri "Tsoro nake ji fa." "Kin jiki, ai sakin jiki zakiyi ki haifo mana babies Masha Allah, yadda bamu da yawan nan kinga ai ma kara yawa a daina mana gori." "Kai Anty." "Allah gori mana,ni da Yaya duk haihuwar daya ce kuma dama kinga mu biyu ne, dangi da yawa na da dadi wallahi sai baka dasu zaka gane, kuma dai haihuwar ce ke sawa a yi yawan." "Tou haka ne." "Tashi kinga kar lokaci ya kara ja mu tafi." "Toh." Ta mike taje ta dauko Hijab dinta ta saka suka fito, Sam na zaune suna ta hira da su Faisal sai ya taso da yaga sun fito yazo suka tafi. Bata shiga wajen Antyn ba direct wajen Yaya ta wuce daga nan sai ta je ta gaida maman ta zauna kamar yadda Anty tace. Dambu nama Yaya take ci da lemo Jiddan ta shigo, ta zata Fauwaz ne har da saurin ta zata boye Jiddan ta ganta. "Auw ashe ba al'murin chan bane nake saurin boyewa." "Rowa dai Yaya,." "Allah ba rowa ba, in dai yagani sai ya dumbuza nan da nan sai kiga ya kare." "Ai Yaya ke da Ya Fauwaz kamar Tom and Jerry kuke,ina wuni?" "Lafiya lou, bismillah ci kad'an." "A ah Yaya, nagode tsautsayi yasa naci ki zo kina yin mafarki na." "Kin wa kanki yarinya." Ta rufe robar ta tura shi gefen kujera tana karkade hannun ta "Babar ku ce tayi min da kanta, naga kwana biyu shiri take nema da kowa a gidan nan, inaga dai tasu ce ta hado shi da Baban naku." "Kai Yaya, saboda haka aka yi miki dambun?" "Allah kuwa ai ina lura da komai, ina kuma shan kallo na..." "Kuma tunda dai ina cin riba sai su karata chan." Ta dora "Hajiya Yaya kenan." "Uhum, ya akayi da magana ne?" "A ah babu, zuwa nayi na ganki kuma mu tafi tare ki kwana mu raba dare muna hirar bankwana." "Allah ya tsareni da zuwa gidan ku wallahi, Allah ya kiyaye ya kaiku lafiya." "Yanzu ba zaki zo muje ki kwana ba?" "Ba zani ba wallahi, kar kuma ki ishen da iyayi bayan ba har zuciyarki kike maganar tafiyar ba." "Allah Yaya har zuciya ta nake yi." "Toh naji, zuwa ne ba zan ba,ehe." "Toh shikenan Yaya, amma zaki rakamu airport din ko?" "Ko gaban gate din gidan nan ba zan rakaku ba bari kiji, salon a hada baki dake a sani a jirgin haka kurum." "Kai Yaya ana tafiya ne ba visa ba komai?" "Oho na sani?" "Toh kuma ai naji zaku je Umrah wannan azumin sannan kuje hajji da babbar sallah, yanzu ya za'a yi kenan?" "A mota zamu ko a jaki." Tace tana gimtse fuska, dariya sosai Jidda tayi har da rike ciki. Tsinken sakace Yaya ta dauka tana sakacen tana hararar Jiddan da take mata dariya "Jakin ne ya ban dariya Yaya, afuwan!" "Kece da kayan haushi ai." "Nayi shiru toh, kinga kar muyi fada tunda dai tafiya zan." "Ba zamuyi ba ai, ya kike fama da dan dunkum din mijin ki kuwa?" "Kai Yaya." "Yo Allah ai sai hakuri irin su." "Na yanzu ba haka suke ba fa Yaya." "Toh ya suke? Ban labari." "A ah, kawai dai suna da kirki da dadin zama in dai ka iya zama dasu." "Ni rashin iya zama da su ne yasa nasha wuya wajen Malam kenan kike so kice." "Ni? Bance ba Yaya, a bar maganar toh." "A barta, dan ni ko Qurani za'a dafa ace min masu irin halin Malam na da dadin zama ba lallai na yarda ba, karshen magana kenan." "Hahaha, karshen magana kenan kuwa Yaya." "Ah toh " "Bari na je na gaida Mama toh, zamu dawo muci dambun naman ni da su Amira." "Wallahi kika gayyato min su tamu ce ni dake." "Dan kad'an zaki sammana." Tace tana ficewa "Karfa ki fara na gaya miki." Ta daga murya, sai kuma ta mike ta dauke robar ta shiga da ita daki ta bud'e cikin kayan ta, ta tura a ciki ta rufe har da saka key sannan ta dawo falon tana sababi. Mama ce kadai a falon da ta shiga, tana zaune cikin ado amma kuma fuskar ta, ta nuna tana dan cikin damuwa, kallon Jiddan tayi sanda ta shigo duk sai taji kunya kafarta ta hau harhadewa ta samu ta karaso ta zube a k'asan carpet cikin tsananin girmanawa ta gaida Maman "Lafiya lou, kuna lafiya?" Ta dora akan amsar gaisuwa "Lafiya kalou alhamdulillah." Jiddan ta amsa cike da mamaki doguwar amsar lafiya lou din da Maman ta baya hade da tambayar lafiyar su bayan a dah lafiya kawai take cewa shima a gajarce tana kin kallon Jiddan "Goben da karfe nawa zaku tafi?" "Da asubah yace." Gid'a kai tayi "Ga kayan ku chan da yace kuna bukata idan kun tashi sai ku tafi dasu." "Ok tam, mun gode Allah ya saka da Alkhairi." "Amin." Shiru ya biyo baya kan Jidda na kasa baki daya falon yayi mata wani irin mugun girma sanyin AC yasa ta sake shiga wani irin yanayi "Akwai wani abun kuma da kuke bukata?" "A ah babu." "Ok! Ki shiga wajen su Amira suna ciki." "Toh." Ta mike ta wuce ciki Maman ta bita da kallo tana son sake gasgata Jiddan a matsayin matar Tariq din ta. A dakin su Amira ta dade suka sha shafta anan taji labarin soyayyar Maryam da Ya Isma'il tayi mamaki sosai ko daya Ya Tariq din be fada mata ba, har Isma'il din ma yazo jiya ya tafi yanzu magabatan sa zai turo sai Ya Fauwaz ma da yake so aje ayi masa tambaya. Suna kyautata zaton kuma Baba dukkan su zai hada har Amira tunda duk dama tsiran su a haihuwa ba yawa sosai Tariq ne dama tsakanin su dukka da tazara me dan yawa sai kuma Ya Fauwaz din ma hakan ne amma su matan a kusa kusa duk Mama tayi haihuwar shiyasa suka taso kusan kai tsaya gaba dayan su. A waya Mama ta kira Amira tace ta turo Jiddan, ta tashi da sauri ta zura Hijab dinta suka dinga mata dariya wai taji kiran suruka ta rikice, tana shigowa falon ta hango shi a zaune yayi crossing kafarsa yana shan abu a cikin mug, kallon k'asa k'asa yayi mata ta, ta yi saurin sadda kanta k'asa ta karasa ta zauna daga gefen Maman a k'asa tace "Gani Mama." "Wai tafiya zakuyi, kunce babu wani abu da kuke bukata ko?" "Babu komai Mama, addu'ar ki kawai muke bukata nothing more." "Toh Allah ya kiyaye ya tsare." "Amin ya Allah." Suka hada baki duk da Jiddan a ciki ciki tayi nata amsawar amma ba karamin dadi addu'ar tayi mata ba. "Ku tashi kuje wajen Babanku." Mikewa yayi rik'e da cup din ita kuma ta dan russuna tace "Mun gode Mama." "Allah ya bada sa'a." ***Jerawa sukayi har part din Baban suka same shi yana waya, Tariq din ne ya fara shiga kafin yace ta shigo, Anty na dakin sa taji shigowar su ta fito lokacin Baba ya ajiye wayar yana duban su "Mutanen turai." Murmushi sukayi dukka har Anty, Tariq yace "Baba barka da warhaka." "Barka dai ango." Ya sake zolayar Tariq din "Baba ina wuni?" Ta gaishe shi a nutse "Lafiya lou 'yata, kuna lafiya?." "Lafiya lou." "Toh madallah, sai tafiya ko?" "Eh." "Toh Allah ya kaiku lafiya ya bada sa'ar abinda aka je nema." "Amin Amin.," Anty tace "Sai a kula sosai, rayuwa irin wannan dole sai kun hada kanku kun yi kuma hakuri da juna " "In sha Allah Baba." "Ka rike amana, bana so naji ko na gani dan Allah. Hauwa'u amana ce a wajen ka " "In sha Allah." "Yawwa, ke kuma ki rike mijinki da kyau kiyi masa biyayya iyakar iyawar ki, Allah yayi muku albarka baki daya ya kade fitina." "Amin." Fitowa sukayi ita ta wuce part din Anty shi kuma yaje yiwa Yaya sallama, daga nan yace ta fito suka je gidan Umaima suka mata sallama sannan suka je gidan Safiyya, anan ne kawai taga ya dan sake har ya zauna ma sun dan taba hira da mijin nata kafin suyi musu sallama suma su wuce gida. #Ranooooo ***❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO KISHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 [11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__** ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_* Page (59) ***Alarm din da ya saita ne na karfe 4 daidai ya tashe su, kallon juna sukayi a lokaci daya sukayi murmushi "Morning Baby." Yace yana janyewa ya sauka daga gadon, "Morning dear.". Tace tana maida masa murmushin. Tashi tayi ta sakko ta nufi wajen kayan su shi kuma ya fice daga dakin. Dan sake gyara kayan tayi sannan ta shiga toilet tayi brush da alwala ta fito tayi raka'atanil fajr ta zauna tana addu'a har aka kira sallar fajr din ta tashi tayi sannan ta cire Hijab din ta fito falon tana tafe tana azkar. Kitchen taje ta sake duba abinda bata sakashi wajen da ya dace ba, ta dan dauraye cups din da Ya Tariq din yasha coffee jiya sannan ta dauko wasu cups din ta dora su akan Iceland ta dafa ruwan tea tasa a flask shima ta dora a wajen sannan ta dawo kan falon a gurguje ta sake gyara shi ta tabbatar komai daidai sannan ta nufi dakin sa. Knocking ta fara yi sannan ta tura kofar bakin ta dauke da sallama. Yana tsaye gaban mirror yana rik'e da bathrobe ta shigo,. "Yanzu zan kiraki dama." Yace yana sakin rigar wankan ya riko hannun ta. "Muje muyi wanka Fauwaz yana hanya tare da yaran chan wai sai sun rakaki dole." "Allah sarki yan uwana." Tace tana murmushi "Oya." Ya kama hannun rigar zai hau cire mata tayi saurin kwacewa "Zan iya." Tace tana dariya "Nima zan iya ai." "Toh na hutasshe ka, kayi wankan anan ni zanyi a daki." "Why? Me yasa?" "Zamu bata lokaci ne." "Ba wani, kawai dai kinsan baki da gaskiya ne." "A ah fa, kaga sauri muke." "Yanzun ma saurin zamuyi, tsayawa ma maganar nan bata time ne." Ya fizgota ya jata zuwa toilet din, ba yadda taso dole ta hakura amma tasan shi ba zai tsaya iya wankan BA wallahi, aikuwa be tsaya din ba haka ya dinga shiriritar dasu har su Fauwaz suka iso, jin gidan shiru yasa Fauwaz kiran Ya Tariq din a waya daga toilet din suka ji kiran, da sauri suka karasa suka fito ya dauki wayar ya kirashi "Muna shiryawa ne gamu nn fitowa." Ajiye wayar yayi suka shirya a tare a gaggauce sannan suka fito yayi falo ita kuma ta koma bedroom dinta ta dan karasa abinda zata karasa sannan ta fito. Tea kawai suka sha shima a tsaitsaye sai snacks din da ta daukar musu wanda Anty ta basu jiya suka tafi. Ita da Amira da Maryam ne a mota daya sai driver shi kuma da ya Fauwaz suma a tasu motar sai wasu motocin biyu har suka isa airport din. Wani kebantaccen wajen suka nufa masu kula da gate din sukayi saurin bud'e musu, suka fito suka shiga cikin building din dake dauke da wani falo a farko sai wani wajn me dauke da round table da kujeru. Falon suka shiga suka zauna suna zama sai ga su Baba nan sun shigo shi da wasu manyan mutane su. Mikewa su Jiddan sukayi bayan sun gaishe su suka koma dayan wajen me round table din suka zauna achan. Suna zaune suna hira kad'an kad'an ya Fauwaz ya shigo yace su taso, jikin ta ne yayi sanyi ta rike hannun Amira suka fito daga wajen, wata hanya suka bi zuwa filin jirgin ba wadda sauran mutane suke bi ba, daga dan baya duk suka tsaya Baba ya dafa kan Jiddan bayan ta durkusa a gaban sa ya saka mata albarka sannan ya mikawa Tariq din hannu suka gaisa yana dan russunawa. Hugging din Fauwaz yayi a karo na farko sannan ya dagawa su Amira da Maryam hannu da suke hawayen rabuwa da Jiddan. Ita kanta hawayen take ta daga musu hannu sannan suka juya suka soma tafiya a jere zuwa wajen jirgin. Sai da suka kai wajen matattakalar sannan suka juyo suka sake daga musu hannu sannan suka haura ciki. "Allah ya tsare ya kiyaye." Baba yace yana murmushi "Uwata kuka kike? Da an kwana biyu fa zaku kai musu ziyara." Yace yana son kwantar musu da hankali. Murmushi sukayi dukka sannan sukayi wa Baban sallama dan daga nan gombe sukayi zasu duba wani aiki. Harabar wajen na cike da mutanen da suka yo wa su Baban rakiya, saukin ta motar tasu tinted ce sai kawai suka hade a mota daya sauran motocin suka bi su a baya suka sulalle daga wajen. ***Personal welcoming suka samu a cikin jirgin kasancewar a first class zasuyi tafiyar me full suite dake hade da private bathroom daga nan akayi musu introducing flight attendant din idan suna da bukatar wani abu. Kujerar su irin wanda ke dauke da pod ne da zaka iya converting dinsa zuwa flat bed hade da fluffy duvets. Gefe kuma amenity kit ne da pyjamas sai slippers. Tafiyar almost 13hours ce zuwa Toronto, kanta na saman kafadar sa cikin yanayin gajiya da kosawa saboda bata taba irin wannan doguwar tafiyar ba, an kawo musu menu sun zaba abinda zasu ci amma bata wani iya ci sosai ba sai juice kawai da sandwich. Gyara musu kujerar yayi suka mike sosai ya lullube su da duvet yana sakata jikin sa sosai. Bacci take ji duk da tana tsoro amma kuma kasancewar tare dashi ne sai taji ta sake sosai har ta soma baccin a jikin sa. Ta jima sosai tana baccin kafin ta farka daidai kusan lokacin da saura kad'an su isa. Gyara mata gefen idon ta yayi da hannun sa ya taimaka mata ta tashi zaune sosai shima ya zauna yana mika mata ruwa tasha kad'an ta maida kanta jikinsa tayi lamo. Bayan wasu mintuna da tashin ta akayi sanarwa isowar su da kuma shirin saukar su. Yanayin fuskar ta ne ya sauya ta nuna farin ciki dan batayi tunanin tayi dogon bacci irin haka ba, ta zata sai ta kara wani zaman sannan zasu iso dan tayi matukar gajiya dan ba akwai comportability a tafiyar amma duk da haka ta jigata sosai amma shi ko kad'an be nuna gajiya ba saboda ba yau ya fara ba. ***Wani irin mugun sanyi taji sanda suka fito waje, dunkulewa tayi tana sake tura hannun ta cikin katotuwar rigar sanyin da ya saka mata. Kafadarta ya kama ya rik'e ta sosai a jikin sa zuwa motar da zasu shiga daga train station din zuwa gida bayan sun bar airport din train suka hau zuwa garin su sannan suka iso. Ko kad'an bata wani ganin gaban ta lafewa tayi kawai a jikin sa sanyin na cigaba da ratsa ta. Tafiya kad'an suka isa gidan nasu da yake a sama, hannun ta duk ya kankare duk da handsocks din da ta saka har guda biyu, shi ya rike mata jakar hannun ta, da sauran kayan nasu, suna kokarin shiga lift Ishaq ya cimmasu shi da Yasmin da suke ta sauri. Wani kallo Yasmin din tayi ma Jidda itama ta dan kalleta kadan kafin ta yi gaba kawai suka shiga cikin lift din dukka. Ishaq ne ya tayashi da kayan. "Welcome back Captain" Yasmin tace tana kallon fuskar sa "Thank you." Yace a gajarce, ya mika wa Tariq hannu alamar ya bashi card din kofar, mika masa yayi yace "Idan kun huta zamu dawo mu gaida Anty amarya." Banza Tariq yayi masa dan ba karamin kular dashi yayi ba, akan me zai taho da Yasmin bayan yasan baya so kuma yasan hakan zai yi hurting din Jidda? Tura kofar yayi ya matsa mata ta shiga ciki sannan yatura kayan nasu yana tare kofar ganin kamar Yasmin din neman shiga take yi "Yasmin muje mu barsu su huta." "Ok." Tace tana kada kanta ta juya cike da tunanin wacece suka zo da Tariq din nata tunda ko da wasa Ishaq be gaya mata yayi aure ba. Suna shiga Jidda tayi saurin hayewa saman gadon ta ja katoton bargo ta lullube har saman kanta saboda yadda take jin kamar ta kankare. Ajiye kayan hannun sa yayi ya karo karfin room heater din nan da nan dakin ya dau dumi sosai a hankali a hankali taji sanyin na barin ta. Zama yayi a gefen ta yasa hannu ya bud'e mata fuskar ta suka kalli juna "Are you feeling better?" Yace yana taba saman forehead dinta "Yes I'm ok, wai sanyi kaman mutum zaiyi freezing?" Dariya yasa "Haka suke kuma kinzo a lokacin sanyin ne shiyasa, amma zaki saba." "A hakan? Ba zan iya sabawa ba." "Zaki saba, baki ga su Ishaq ba? Kamar ma ba sanyin ake ba." "Matar sa ce dayar?" Ta tambaye shi tana kallon fuskar sa "Itace Yasmin!" Yace yana dago kanta ya dora a saman cinyar sa, shiru tayi tana hango haduwar Yasmin din da mugun wayewar ta. kamshin turaren ta har yanzu yana mata yawo a hanci kana ji kasan irin designer perfumes din nan ne masu shegen tsada da kamshi. "Don't worry zan yima Ishaq magana akai, I don't want any problem." Bata ce komai ba, tana jinshi yana zare mata scalf din kanta, sannan ya janye kan nata ya dora a saman pillow ya mike ya wuce toilet yaje ya hada ruwa me zafi a cikin tub yazo ya mikar da ita "Muje ki rage gajiyar nan." Tashi tayi ya ja hannun ta zuwa toilet din duk tayi sanyi sosai, shi da kansa ya cire mata kayan jikin ta ya bar mata na cikin kawai dan baya so ya kara mata wata gajiyar akan wadda take ciki. Fitowa yayi ya barta a ciki tayi wankan ta fito ta shafa mai ya taimaka mata ta saka kaya masu dumi sosai sannan ya shiga toilet din shima yayi wankan hade da alwala yazo sukayi sallah daidai lokacin da order din da yayi ta iso ya fita ya karbo ya kawo musu suka ci abincin. Bacci kawai take so tayi dan idon ta har lumshewa yake tana gama cin abincin taje tayi brush tazo ta kwanta ya dan kalleta yana Jona system dinsa dan yana saka sim din sa har ya samu kira amma be daga ba sai ya jona system din ya zauna yana dubawa abubuwan da suka turo masa wanda zai fara gobe as early as 8am. Cikin bacci taji ana gyara mata kwanciyar ta, ta dan bud'e ido kad'an ya rungume ta yana rufa musu blanket din dukka jikinsu. *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ 400 *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ 400 *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ 400 *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ 400 *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ 400 *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 2k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_* [11/25, 3:55 PM] Rano2: _SL__** ©️®️*_*_Hafsat Rano_*_*               Page (60) ***Tun da sukayi sallar asubah ta koma bacci, be fada mata zai fita ba dan yaga alamar a gajiye take tikis har lokacin sai bin gefen gado take karshe ta haye tana jan duvet ta rufe kanta nan da nan kuwa tayi bacci. A nutse ya shirya cikin shigar farar shirt me layin baki daga saman shoulder din, navy blue dogon wando sai light blue tie. Be saka jacket da cap din ba sai ya ajiye su a gefe ya gyara zaman waist belt dinsa sosai ya shiga dan madaidacin kitchen dinsu ya samo coffee yasha kad'an sannan ya fito ya saka dark blue din sau ciki ya dauki briefcase dinsa ya dora cap din akan sa ya rike jacket din a dayan hannu ya zo daidai kanta ya durkusa kad'an yayi mata peck a gefen kuncin ta, ya ajiye mata note a gefen gadon ya fice da dan sassarfa.   Cikin bacci taji kamar ana taba kofa, ta bud'e idonta kad'an tana wurwurga idon ta a dakin tana neman sa, baya nan sai ta sakko da sauri ta fito falon nan ma baya nan. Kofar taje ta bud'e a zaton ta ko shine ya dan fita sai taga Yasmin a tsaye taci uban kwalliya rike da basket me kyau a hannun ta. "Goodmorning." Tace mata tana rabawa ta shiga cikin gidan kai tsaye, sakin kofar Jidda tayi tabi bayan ta tana jin duk ta muzanta dan ko brush batayi ba bare wanka. "Captain fa?" Tace tana kallon falon "Oh yau fa dole ya fita da wuri na manta, oops ya akayi na yi late har ya fita? Allah yasa ma yayi breakfast dan nasan yau kam zai zama so busy." Kallon ta kawai Jidda take bata ce komai ba amma maganganun ta sun dan taba ta, kenan fita yayi amma ta share baki tana bacci babu wanka bare tayi tunanin samar masa abinda zai karya. "Kanwar sa ce ke amma ko?" Tace tana zama bayan ta gama karewa falon kallo "Umm." Jidda tace tana kokarin barin wajen "Very beautiful kamar shi, amma fa ya fiki kyau." Tayi dariya, yak'e Jidda tayi ta wuce kawai ciki ta barta a falon bakin ciki na tirnike ta, daga zuwan ta? Sai ta fara cin karo da irin wannan masu budadden idon? Tana daki tana jin motsin ta a falon ko me take yi oho, wanka ta tashi ta shiga ta dauko wani kaya da take tunanin da BA zata iya sawa ba saboda da kunya amma da taga irin shigar da Yasmin din tayi cikin wani matsattsen jeans da riga ta saka turban kawai akanta ko mayafi babu yasa ta ji itama zata iya.   Wankan tayi ta fito ta shirya cikin rigar da ta kasance red colour ta shafa kalolin turarurruka masu kamshin gaske harda wani hadin khumra da Anty ta siya mata a wajen wata mata. Rigar da kadan ta wuce guiwar ta sai ta saka socks me dan tsawo ta gyara gashin kanta ta saka hair band ta fito da gashin ta tsakiyar kan. Light makeup tayi ta shafa red jan baki sosai wanda ya sake fito da sihirtaccen kyawun ta. Rigar daga saman wuyan an dan tsaga ta sai ta dora farar karamar rigar sanyi irin me gashin nan.   Yunwa take ji sosai, ragowar abincin da sukayi order jiya ta tuno ta fito falon, Yasmin na zaune tana kallo a TV tana danna waya ta saki baki ganin Jiddan, kin kallon ta Jiddan tayi ta wuce kitchen din da yake cikin falon Yasmin din na kallon ta tunda ba wai a rufe yake ba, fridge ta bud'e ta dauko abincin tayi warming dinsa a microwave ta zubo a plate tazo ta zauna a kujerar dake facing dinta ta shiga cin abincin a hankali. "Ya sunan ki?" Dagowa Jidda tayi ta kalle ta, "Na'am?" "What is your name? Sannan menene alakar ku da Tariq?" "Jidda, alakar mu kuma wannan shi zaki tambaya ai." "Me yasa?" "Zai fi iya fada miki ai." "But baya tsayawa ya saurare ni ai, ni kadai nake son shi amma shi ko kallo ban ishe shi ba, please i need your help." Wani kallo Jidda tayi mata irin kallon baki da hankali din nan, sannan tayi dariya kawai tana cigaba da cin abincin ta dan ta lura sam Yasmin din bata da hankali. "Please kanwar mu, wallahi inason shi sosai." "Naga alama ai, ki sameshi kawai kiyi masa magana nima tsoron sa nake ji." "Ba zaki iya ba?" "No ba zan iya ba." Tace tana mikewa, taje ta wanke plate din ta gyara wajen ta dawo falon ta zauna tayi connecting wayarta da wifi ta kira Amira facetime, lokacin su kusan biyar din yamma. Bata daga ba sai kawai ta mike ta dan kalli Yasmin din tace "Ki gaida gida ni na shiga ciki." "Tafiya zan nima, idan ya dawo kice nazo, ga breakfast dinsa nan hade da lunch zan kawo dinner." "Chef ce ke?" "Yes." Tace tana murmushi "Ok yayi." Tace tana yin gaba, ita kuma Yasmin din ta mike sai gashi ya turo kofar ya shigo, tsayawa chak Jidda tayi jin an budo kofar wanda ta tabbatar da shine, kayan jikin ta, ta kalla kunya na kamata amma sai ta daure ta cije ta juyo tana fuskantar sa., Takalmi yake kokarin cirewa ya lura da Yasmin din dake tsaye a falon nasu, sai Jiddah ta ya kalleta ya sake kalla kafin ya tabbatar da itan ce ko wata ce daban saboda tsabar kyawun da yaga tayi masa. Da wani irin salo da bata san ta iya shi ba, ta nufe shi ta karasa da dan sassarfa ganin yadda yake bin ta da wani irin kallo, rungume shi tayi da sauri ya saki jakar hannun sa yana kankame ta sosai a jikin sa. "Welcome home baby." Tace tana ciro kanta daga kirjinsa, kin cikata yayi yana shakar kamshin turaren da take yi cikin wani irin yanayi "I missed you so much." "Ba kai ne ka tafi ka barni ba?" "I'm so sorry kinji? Bana so na tashe ki ne naga kin gaji sosai, shiyasa amma dama ba dadewa zan ba." "Tom shikenan na hakura." Tace tana masa murmushi "You look very beautiful." Yace yana kallon kayan jikin nata, murmushi tayi ta duka ta dauki briefcase din tasa ta rike hannun sa "We have a visitor." Tace tana nuna masa Yasmin dake tsaye kamar gunki. "She's not welcome here." Yayi mata whispering a kunne. "Yasmin welcome, meet my beautiful wife Jidda." "Oh,okh yayi, Allah ya bada zaman lafiya. But she's young!" "Young and sweet." Yace yana kissing hannun Jiddan da ke cikin nasa. "Bari na wuce, Allah ya taimaka." "Amin mun gode." Jidda tace tana mata murmushi "Kin manta basket dinki." Tace mata ganin zata fice, banza tayi ta karasa ficewa da sauri. Kicibis sukayi da Ishaq sai kawai ta fashe masa da kuka "Subhallahi, me ya faru Yasmin?" "Ishaq Tariq sam bashi da tausayi, ashe aure yayi? Duk yadda nake son shi me yasa baya so na? I'm I ugly? Or what?" "Calm down, kinsan akwai differences tsakanin ki da Tariq, beside be taba furta miki kalmar so." "Na sani, kuma I'm 100% ok with that hoping zai iya so na ko gaba ne, amma saboda tsabar wulakanci kaga abinda sukayi min shi da so called wife din shi?" "Kiyi hakuri please, bari zamuyi magana dashi." "There no need Ishaq, na hakura wallahi." Sai ta juya da sauri ta bar wajen. girgiza kai yayi ya fasa zuwa wajen Tariq din kawai ya bi bayan ta.   ***Yana zaune kamar sarki ta cire masa tie din ta kawo masa ruwa yasha sai ya jawota kan kafarsa ya manna kansa a jikinsa "Kin yi kyau Jidda na,and naji dadin yadda kika fahimce ni, kuma kika yi treating Yasmin yadda ya kamata ba hauka ba zubar da class, she mean nothing to me kuma itama ta sani, Ishaq ne duk yayi complicating abun yana bata false hope bayan yasan ba haka bane ba" "Allah sarki, sai dai tayi hakuri." "Tariq naki ne ke kadai ko?" "Yes!" Ta gida masa kai "Good." Yace yana dariya "Mine and only mine." Ta dora tana tashi daga jikin sa rike da tie din nasa. Jawota yayi ya maida ita ta zauna "Then give me cin hanci idan kinaso na zama yours baki daya." "Me kake so?" "Anything special." "Ok an gama ranka ya dade." "Wow! Sai ni dan gata." Yace yana matso da fuskar sa tata, yasa baki akan lips dinta ya shiga tsotsa a hankali in a passionate way. ***Rayuwa me dadi da inganci suke yi a tsakanin su cike da kaunar Jun, Tariq baya shakkar nunawa kowa irin kalar soyayyar da yake mata musamman yanzu da suke kasar masu jajayen kunnuwa da babu wanda zai damu da abinda kake ciki ko kayi. Tare suka je ya bawa Yasmin hakuri dan ko yaya ne mutumin da yace yana son ka yafi wanda yaki ka, ashe ma tun ranar da abun ya faru Ishaq ya shigar da kansa wajen ta, and she accepted saboda dama sun shaku sosai.   Duk da busy schedule din Tariq haka yake kula da Jiddan sosai kuma kullum a gida yake kwana tunda har yanzu be fara zama irin so busy din nan ba. Duk abinda zai yi within kasar yake ya dawo amma dai daf yake da fara fita wasu kasashen anan ne kuma dai dole Jidda tayi hakuri, be taba jin yana da second option a aikin nasa ba sai da ya tabbatar dole watarana ya dinga tafiye tafiye sosai kuma ba tare da Jiddan tasa ba.    Wajen taran dare ya shigo gidan a gajiye tikis yana hanya sukayi magana da Fauwaz akan maganar auren sa da aka tambaya wanda Baba yace dukka zai hada harda su amira tunda itama ta samu mijin maryam dama Ya Isma'il ne, da murnar sanar mata ya shigo gidan amma sai ya sameta a kwance ta lulluba da bargo tana rawar sanyi, da sauri ya yaye mata bargon ya durkusa a gaban ta "Subhallahi, menene?" Yace yana dagota jikin sa "Zazzabi nake da amai." Tace tana rufe idon ta saboda tsabar yadda ta galabaita dan kusan sau ashirin tana amai. "Shine baki kirani ba? Kinga yadda kika galabaita?" Yace yana cire blanket din saboda yadda zazzabi ya rufe ta sosai. Ruwa ya debo a tap me dumi yazo ya rurrufe dakin sosai yazo ya jawota jikin sa ya janye rigar ta ya shiga goge mata jikin da yayi zafi sosai. Sai da yaga zazzabin ya dan daidaita sannan ya shiga ta wayar sa yayi booking appointments na ganin Dr ya zabi 1hour sannan ya gyara mata jikin ta suka tafi asibitin.    Suna zuwa akayi mata duk gwaje-gwajen da za'a mata aka tabbatar she's pregnant, tsabar murnar be san sanda ya dagata sama ba, dariya Dr din ta dinga musu sannan ta basu maganguna suka dawo gida. Tun daga lokacin shikenan kuma laulayi ya fara me matukar wahalarwa, duk sanda zai fita kamar zai mata kuka saboda tausayin ta,amma sai ta karfafa masa guiwa ta samu ya fitan baya dadewa sosai yake dawowa sai kuma washegari. Da haka har cikin yayi kwari sosai,daidai lokacin bikin su Ya Fauwaz, be so ba dole yace ta fara shiri ya kaita gidan saboda shima aikin nasa ya fara matsawa sosai dan zai iya tafiya yayi kwana biyu ko uku ma baya nan, kuma ko ya dawo ba zai fi yan awowi ba zai sake tafiya. Murna sosai ta hau yi dan batayi tunanin zasu je gida nan kusa ba, shi kansa be yi tunanin hakan ba amma gwara gidan da ta zauna anan din babu kowa shima ba zama yake ba ga ciki kuma. ***Kwana biyu da maganar tafiyar ya siya mata ticket ita kadai dan bazai samu damar zuwa ba kuma, duk bashi da walwala ganin haka yasa ta nuna murnar ta duk da itama a gefe daya bata san yadda zatayi coping idan babu shi ba, ya riga ya saba mata da caring dinsa haka dole zata sha famar rashin shi.    Ana gobe zata tafi ya kanainaye ta dan tun magriba ya dawo gidan ya hanata sakat duk in da ta motsa yana manne da ita, ji yake kamar yace ya fasa aikin nasa kawai su tafi tare su koma gida suyi normal rayuwar su amma ya zai? Da k'yar ya barta ta karasa hada kayan da zata tafi dasu suka yi dinner yace bacci yake ji ta san sarai kuma ba wani bacci rigima ce irin tasa gashi ita yanzu sam bata san abinda yake so din amma shi kamar wanda aka kara ingizowa baya taba barin ta abu kad'an tayi sai yace tayi turning nashi on, haka dai take daurewa yanzun ma haka ta daure dai dan ta lura da duk take-taken sa zai iya canceling tafiyar yace sai wani lokacin shiyasa take ta lallabawa tana bin sa yadda yake so din.    Ita ta fara tashi da safe bayan sun yi sallar asubah maimakon ya barta ta karasa abinda zata karasa kafin su tafi amma ya ki barin ta, ya rike ta kam yana tura kansa cikin rigarta wajen da tafi komai daukar hankalin sa yanzu a jikinta saboda yadda suka kara girma sosai. Bata hanashi ba duk da ta kai karshe amma haka ta taimaka masa ya samu abinda yake so sannan sukayi wanka tare suka shirya. Zai wajen azahar sannan suka fita zuwa airport din suna zuwa yayi mata duk abinda zai yi, ya rakata har cikin jirgin yana rik'e da ita, sai da ta zauna sosai tana kallon sa yayi hugging dinta so tight a hankali ya rad'a mata "Ki kula min da kanki da babyna " "In sha Allah." "I love you so much Jidda nah." "I love you too." "Allah ya kiyaye, call me da kun isa dan Allah " "I will, in sha Allah." Tashi yayi ya juya ya fice ganin saura kadan jirgin ya tashi, yana tsaye daga gefen wajen jirgin ya soma tafiya a hankali a hankali har ya daga sama, ya sauke ajiyar zuciya yana komawa ciki dan shine zai dauki next passengers din da zasu tashi zuwa Manchester.    ***Kasancewar ba wannan ne tafiyar farko ba sai taga dan saukin tafiyar duk da shima ta galabaita, san gefen ta akwai wasu couples da yaran su,su biyu kuma yan Nigeria ne sune ma suka zama kamar yan uwanta. Matar me suna Amrah da Mijinta Sultan (Abinda Ke Cikin Zuciya) sai yaran su biyu, sun burgeta sosai saboda yadda suka shaku da junan su kuma yadda sukeyi ita da mijin nata ya kara sa mata kaunar Ya Tariq dinta tana hasaso suma sun zama haka watarana. Exchanging contacts sukayi da matar daidai lokacin da suka iso filin jirgin na Abuja. Mama ce da kanta tazo daukar ta, tunda ta samu labarin cikin Jiddan take cike da matukar farin ciki, sun dade da shiryawa da Baba kuma tsakanin ta da Anty babu laifi kadaran kadahan Yaya ce dai take shan gata daidai gwargwado a wajen ta.    Mamakin Jiddan ne ya dadu sanda suka fito taga Maman a tsaye tare da Amira da Usman suna jiran ta, da sauri Amira ta taho zata rungume ta Mama ta daka mata tsawa "Baki da hankali ne? Baki ga halin da take ciki bane ba?" Kunya ce ta kama Amiran ita kuma Jidda ta dinga dariya ta karaso ta russuna zata gaida Maman tace Maza Maza ta mike ba'a son me ciki da durkuso,tashi tayi a kunyace ta gaida Maman ta amsa tana kallon cikin nata. ***Rayuwa ce ta cigaba da garawa cikin ikon Allah har cikin Jidda ya shiga wata tara, an yi bikin su Amira Wanda Jidda ta zama itace akan komai dan hatta Mama ita ta barwa ragamar komai duk abinda zatayi sai ta nemi shawarar Jiddan wanda take cike da kaifin tunani hakan ya sa ta kara shiga zuciyar Maman sosai.    Yaya ce tazo ta zauna da ita da k'yar sanda ta shiga wata takwas dan sai da Baba yasa baki sannan ta yarda tazo suka zauna. Waya suka gama kenan da Ya Tariq yace ta tashi ta fita ta dan zazzagaya gidan saboda tace masa bata jin dadin jikinsa. Yunkurawa tayi da nufin tashi taji wani abu ya soke ta da sauri ta durkusa ta kwala kiran Yaya.  Tare suka shigo da sabuwar me aikin ta da mama ta kawo mata bayan Godiya, da sauri ta fita tace a kunna mota dan har Jiddan ta kai kasa saboda wani irin murdawa da cikin ta yayi ga wani irin ciwon mara da ya taso mata gadangadan. Yaya ce ta riketa tana mata sannu, Godiya taje da sauri ta sau waya ta kira Aunty ta fada mata, sai ta aika Usman tace ya fadowa Mama aikowa mayafi kawai ta yafa ta fito, kafin taje sun wuce asibiti sai ta bisu chan din.   Cikin ikon Allah ana zuwa ba'a fi minti talatin ba Jidda ta haihu haihuwa me sauki kuma lafiya lou dan ko karuwa batayi ba. Murna a wajen Mama tayi saurin kiran Anty t fada mata sannan ta kira Baba shi kuma ya kira Tariq yana tsaka da shirin tahowa dan ranar zai baro kasar sai ga kyakkyawan labari. Sujuduj shukur yayi yana kara godiya Allah da ya sauke ta lafiya. Mace aka samu me kama daya sak da Jiddan har farin kamar dai yadda Tariq din kullum yake jaddada mata me kama da ita yake so. Nan da nan asibitin ya cika da su Anty, Amira, Ya Safiyya da babyn ta haka ma Umaima, Ya Fauwaz da matarsa. Maryam ce kawai bata nan tana Kano amma an kirata an fada mata. Baba ne yazo yaga sabuwar amaryar tasa wadda Yaya ta rike ta kam ta hana kowa sai dai Ka kalle ta a hannun ta, Baba kawai ta bari ya dauka shi da abokin sa amma daga su bata sake barin kowa ba. Kasancewar kalou aka haihu yasa basu kara awa daya ba aka sallame su. Gida aka wuce da ita part din Mama in da dama tun kafin haihuwar tasa aka gyara mata dakin dan so take ta kara wanke kanta a wajen Tariq din da Baba har ma da Jiddan. ***Tana zaune bayan anyi ma jarirriyar wanka yamma Mama tazo tace ta taso ruwa ya yi, tashi tayi ta dora towel a saman kanta ta shiga toilet din, Maman ce da kanta tayi mata wankan towel din ta gasa masa jikin ta sosai sannan ta nuna mata yadda zatayi tsarki sosai, ta fita ta barta taje ta kunna bunner a dakin sai ga Anty ta shigo ta dauki babyn ta fito da ita falon wajen bakin da akayi. Farfesu me zafi aka kawo mata Maman da kanta tasa ta taci sosai sannan ta bata magungunan ta tace ta kwanta ta huta sosai ta fita ta jawo mata kofar dakin. Ta dade sosai tana baccin cikin baccin taji kamar ana shafa mata fuskar ta, bud'e idon ta tayi dake cike da bacci ta ganshi yayi kneel down a gaban ta yana kallon ta cike da tsantsar tausayin ta. Da sauri ta tashi tana bude baki, sai ta rungume shi cike da farin cikin ganin sa "Jidda nah!" Ya furta yana kara rungume ta sosai "Thank you so much, nagode nagode nagode, kin gama min komai a duniyar nan da kika haifa min Princess dita." Gefen ta, ta kalla jarirriyar na ajiye a kusa da ita tana bacci, ya dade da shigowa yana kallon su cike da so da kauna, ji yake kamar ya hadiye su saboda kauna. "Kin ganta ko? Kamar ku daya har idon naki ne Baby." "Haka nima nake?" "Sosai." "Amma kalli fingers dinta irin naka ne." "Na gani Jidda, Allah kenan, Allah ya raya mana ita yayi mata albarka, I love you so much." "I love you so so so much." Ta maida masa tana sake hugging dinsa "Kayi mata huduba?" "Yes! Na saka mata Halimatussadiya." "Da gaske?" Ta waro idon ta "Da gaske, Anty ta chanchanci fiye da haka." "Nagode nagode nagode mijina." "Shssh, babu godiya a tsakanin mu, ina sonki sosai fiye da yadda nake son kai na, zan iya yin komai saboda farin cikin ki." "Inason ka sosai, beyond words! Allah ya barmu tare har karshen rayuwar mu." "Amin Ya Allah!" "What next?" Yace yana bude hannun sa "A very beautiful beginning in sha Allah." "Zaa bude sabon chapter rayuwar Jidda da Tariq." "In sha Allah." Tace tana sake kwanciya a jikin sa. ALHAMDULILLAH!!! TAMMAT!!! *_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_* *ZAFAFA BIYAR BACTH A* 1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350 *(Bilyn Abdul)* 2.. _KAI MIN HALACCI_ 350 *(Miss xoxo)* 3.. _BURI DAYA_ 350 *(Mamu gee)* 4... _DAURIN BOYE_ 350 *(Huguma)* 5... _SAUYIN KADDARA_ 350 *(Hafsat Rano)* _Duka biyar 1500_ *___________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH B_* 1... _DAURIN GORO_ 350 *(Hafsat Rano)* 2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350 *(Huguma)* 3... _QAUNAR MU_ 350 *(Mamu gee)* 4... _IGIYAR ZATO_ 350 *(Miss xoxo)* 5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH C_* 1... _MIN QALB_ 350 *(Mamu gee)* 2... _SARAN ƁOYE_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _KIBIYAR AJALI_. 350 *(Miss xoxo)* 4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH D_* 1... _ALKIBLA_ 350 *(Huguma)* 2... _DALAAL_ 350 *(Miss xoxo)* 3... _UBAYD MALEEK_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350 *(Hafsat Rano)* 5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350 *(Bilyn Abdull)* _Duk biyar 1500_ *____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH E_* 1... _SO DA ZUCIYA_ 350 2... _TAKUN SAAKA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 3... _HALIN GIRMA_ 350 *(Hafsat Rano)* 4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350 *(Huguma)* 5... _DEEN MARSHALL_ 350 *(Mamu gee)* _Duk biyar 1500_ *______________________________* *_ZAFAFA BIYAR BACTH F_* 1... _BAKAR INUWA_ 350 *(Bilyn Abdull)* 2... _RAYUWAR MACE_ 350 *(Hafsat Rano)* 3... _NOOR ALB_ 350 *(Mamu gee)* 4... _MASARAUTA_ 350 *(Mss xoxo)* 5... _KUFAN WUTA_ 350 *(Huguma)* _Duk biyar 1500_ *_____________________________* *_ZAFAFA BIYAR BATCH G (Da ake kanyi yanzun)_* 1... _FARHATAL QALB_ 400 *(mss xoxo)* 2... _GURBIN IDO_ 400 *(Huguma)* 3... _SANADIN LABARINA_ 400 *(Hafsat Rano)* 4... _INAYAH_ 400 *(Mamu gee)* 5... _BABU SO_ 400 *(Bilyn Abdull)* _Kuɗinsu a yanzu 2k duk biyar_ *YADDA ZAKU BIYA NAKU KUDIN BOOKS DIN:* _ACCOUNT NAME:_ *HAFSAT UMAR KABIR* _BANK NAME:_ *ZENITH BANK* _ACCOUNT NUMBER;_ *_2270637070_* _SAI A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA:_ *_07040727902_* _IDAN KUMA KATIN MTN ZAKU TURA KO VTU SAI A TURA TA:_ *_09134848107_* *_Muna godiya da zaɓin zafafa biyar 😘😘😘🙏🏻_*