*SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* 🌻🌻🌻 _"Ƙungiyar Marubuta masu tasawa, Rubutunmu shi ne tafiyar da ke wuce lokaci, mu ne masu ɗaukar harshen gobe a yau. Marubuci ba ya zana kalma kawai, sai dai ya zana mafarki a zuciya, ya maida shi haske ga al'umma. Wannan shi ne alwashinmu a matsayin mu na matasan marubuta. Taken mu shine ɗaga darajar Marubuta masu tasawa."_ 🌻🌻🌻 🌻SYou Na sadaukar da wannan littafi ga ’yan’uwa marubuta na cikin ƙungiyarmu mai albarka — *Future Writers Association*. Ku ne ginshiƙin kwarin gwiwa da hasken tafiyata a duniyar rubutu. Wanan Littafin yafi ƙarfin Shafi ko alƙalami; wani ɗan ɓangare ne daga zukatanmu da ke ɗauke da mafarki, ƙalubale da burin da muke fatan cimmawa tare. Allah ya ka ɗorar mana da haɗin kai, ka bunƙasa ƙungiyarmu, ka ba mu ikon sauya al’umma ta hanyar kalmomi. *–Fatan alheri da ƙauna.* *[Sayyid writer Legend]* بسم الله الرحمن الرحي SHAFI NA FARKO (P. 01) Durƙushe nake, gaban kawu Mudi yana zubamun bulalal da nake jinta kamar saukar ruwan dalma a jikina. Yata ƙarƙare sai zubumun bulalal yake iya ƙarfinsa, idanuwa na suna a murje kamar baza su zubar da hawaye ba. A cikin raina kuma faɗi nake. “Ya ubangiji ka gama Mus’ab da masifar duniya, da ta lahira. Ya ubangiji kasa yayi saɓani da Alkhairi, yayi ido huɗu da tsautsayi , da asara.” Wata bulala da ta shigeni ce, tasa ƙwalla fitowa daga idona ba tare da na shirya ba. Da sauri nayi ƙasa dakaina, ina goge ta da hijabi na. Mai na yiwa Mus’ab a duniyar nan ya tsane ni har haka?, a kullum burinshi yaga ana jibgata kamar sabuwar jaka, ko nace tsohuwa tunda na saba da dukan. Tabbas nasan, ina da taurin kai, da kafiya, haka naci, amma kwata-kwata bani da rashin kunya. To yanzu ma ko ina da rashin kunyar, zan tsaya a waje na fara yiwa mutane rashin kunya ba tare da sunyi mun komai ba. Mahaukaciya nake ko me?, su kuma iyayen tarbiya, gidan da yafi na kowa tarbiya. Daga ance musu gani can waje, ina yiwa mutane rashin kunya. Shine zai sani gaba da duka. “Tashi ki bani waje.” Muryar kawu mudi ta shiga kunnuwa na, tashi nayi na nufi cikin ɗakin mu. Nasan Mamana ba zata ce mun ko sannu ba, hakan yasa na kwanta kan doguwar kujera, ina kuka na a hankali, zuciya ta cike da ƙarin tsanar Mus’ab. Ƴan mintina kad’an, Sadiya da Ummi suka shigo ɗakin namu, lokacin Mamana na cikin d’aki. “Gaskiyya Yaya Mus’ab baya kyautawa, kullum shi burinshi yaga an dake ki, ko da yaga kina yin rashin kunyar ai shi mai yi miki faɗa ne.” Wani haushin Ummi ya ƙara kamani, ita yayanta bazaiyi ƙarya ba kenan, sai nice nake ƙarya tunda gashi sun yarda nayi rashin kunyar. Ni daga ganin mutane, suka tambayeni gidan Alhaji Idi me mai. Na nuna musu gidan, d’aya cikin su yace. “Mungode ‘yan mata.” Ni kuma nayi dariya shikenan kawai sabida Mus’ab ya tsaneni, yasa aka jibgeni kamar ba daren jiya yasa Yaya Iliyasu ya mareni ba. Sadiya ce, ta bawa Ummi amsa. “Nikam gaskiyya abinda Yaya Mus’ab yake yayi yawa, shi fa bazai hanamu abu ba, sanan bazai sa a hana mu ba. Ita kad’ai yake sawa a daka, itama kuma ba sabida soyayya ba, sai dan ‘yar tsamar dake tsakanin su. Duk gidan nan Yaya Mus’ab ne kawai ke nuna ware, yana nuna ku kaɗai ne ƙannansa, kuma sauran yayin mu ba haka suke ba.” “Sadiya gidan ku da wanan maganar, kar nasake ji kinyi ta. Gaba ɗaya gidannan babu wani mai ware, domin dukkan ku jini ɗaya ne, Hajja itace asalin ku. Kuma shi Mus’ab ai yanayin sa ne a haka, bai da son mutane kwata-kwata.” Ummanah dake cikin ɗaki ta faɗa. Nikam takaici ya isheni, na yadda Ummanah bata taɓa jin haushin Mus’ab, juya musu baya nayi na kwanta. Tun ina jin maganarsu sama-sama har bacci ya d’auke ni, zuciyata cike da tsanar Mus’ab. Ƙarfe 1:45 dai-dai natashi, domin nasan da zuwa islamiya hakan yasa natashi a lokacin. Banɗaki na shiga na watsa ruwa, tare da ɗaura alwala na fito na tada sallar azhar. Ina idarwa na shiga Kitchen na lodo abinci, dan gaskiyya babu laifi Allah ya horemun ci, kamar yadda Mus’ab ke dizgani cikin mutane. Yake cemun (Gara uwar ci). To kam gaskiyya ina da cin abinci, sai dai kuma idan naci yanzu fa zai iya zama naci har na dare, dan bani da yawan cin abinci akai-akai, lokacin farko dai xanci har sai yabawa mutane mamaki. Ina gama ci na zura hijabi na, nayi makaranta, a tsarin gidan mu (Gidan Galadima) duk lokacin tafiya makaranta sai an shiga ɗakin Hajja, an gaida ta, kama da makarantar safe, rana, da kuma ta dare, sabida ɓacin rai da hausin ɗan gaban goshinta, wanda nafi tsana sama sa kowa a duniya yasa nakaɗa kai na tafi banje na gaida ta ba. Ko a islamiyyar ma haka na zauna, kamar wacce aka yiwa mutuwa. Tsana da haushin Mus’ab na lugude a zuciyata. Ko da na dawo ma banje ɗakin Hajja ba, ɓangarenmu na nufa nayi kwanciyata. A ɓangaren Hajiya Hajja kam, tana ganin kowa na shigowa gaisuwar tafiya amma babu ni, babu alamu na. Hakan ya matuƙar damunta, tana nan zaune ‘yan islamiyya suka fara dawowa. Ganin sun ƙare babu ni yasa tace da Iki. “Ikirama, kira mini Salame.” Tashi Iki tayi ta nufo ɓangarenmu, ina kwance kan doguwar kujera tashigo ɗakinmu. “Salma, kizo inji Hajja.” “Kice mata banzo ba….” ban ƙarashe ba, naji an make mini baki tare da faɗin. “Zanci ubanki Wallahi, Hajja kike cewa ace baza kizo ba. Sai kin ƙara tabbatar da cewa baki da kunya ko.” cuṅo baki nayi gaba, tare da sakkowa daga kan kujera, banko ɗauki mayafi ba na fice. Dabda ɓangaren Hajja, na hango Mus’ab yana tafiya a hankali, kamar wanda ƙwai ya fashewa a ciki. Idanunshi sunyi jazur, kamar gauta. A fili nace. “Allah yasa wanan ciwon kan ne ajalinka.” A bakin ƙofar ɗakin Hajja na tsaya, tare da cewa. “Gani.” “Naganki tijararra, naganki.” Juyawa nayi zan koma ɓangaren mu, ba tare da na ce ko ƙala ba, tunda ni yau bakina jinshi nake kamar an ɗora masa kwaɗo, babu abinda nake ji sai tsanar Mus'ab, Hajja ta ƙara cewa. “Yanzu salame, tafiya za kiyi.” “Toh Hajja mene zance miki, bayan wanan kafirin la’ananne jikin naki, yasa ‘ya’yanki suna dukana, sun mai dani kamar wata jaka, kowacce a ka siyo.” “Yanzu Salame,Mus’abun kike kafurtawa, har da la’ana. To fice ki bani waje.” “Daman bani na kowa kaina ba, kice kika nemeni.” na faɗa tare da fice, a hanya na ƙara cin karo dashi, har yanzu bai kai ga shigowa ba. Dogon tsaki naja tare da cewa. “Duk wanda ya ɗauke zalunci a matsayin sana’a, rayuwarshi zata ƙare a jinya.” nikaina nasan da’a ce ba'a wanan halin Mus’ab yake ciki ba, da kafin na ƙarashe wanan maganar na kwashe haƙora na a hannu. Ci gaba yayi da tafiyarsa, nima nayi ɓangarenmu, a raina ina nanata addu’a ta ‘yar kullum. “Allah yagama Mus’ab da masifar duniya.” *Asalinmu* Dafarko dai sunana: Salamatu Yunusa Galadima. Kakan mu shine Galadiman, bawai Galadima na fadar sarki ba, a’ah sunane kawai yace. Mahaifina Yunusa shine ɗa na Uku wajen Galadima, Yakubu shine babba, wanda muke kira da Abban ciki. Sai kuma Aisha wacce muke kira da Mami, sai Mahaifina Yunusa wanda kowa ke kiranshi da Abba, sai kuma Halima wacce ake kira da Ummah, sai Abbas da ake kira da Alhaji ƙarami, daga shi sai Ilyasu da ake kira da yaya Ilyasu, shi kam shine baya son ace masa Kawu, shiyasa ake ce masa, Yaya ilyasu, sai kuma autan su Kawu Madu. A taƙaice da Galadima kakanmu yana da ‘ya’ya bakwai, maza biyar mata uku. Kuma duka wa’yan nan ‘ya’yan sun fito daga matarsa guda ɗaya, (Hajiya Hajja). Kakanmu Galadima, tsohon mai kuɗi ne. Domin ko gidansa wanda muke ciki yanzu, yana da girman da kowanne part zau dauke mata hudu. Kafin rasuwarsa shiya bawa kowa ɓangaren da zai zauna, domin bayason yaga yaranshi su raba giadaje. Yace yana da burin ganin mun tashi a zuri’a ɗaya. Abban ciki ne ya fara aure, matarshi yar kano ce mai suna Jamila. Muna ce mata Maman ciki, idan mutunci yana yawa to ya yiwa Mamam ciki yawa, tana son mu, tana kaunar mu. Duk abu indai Maman ciki ce bata taba ware mu da yaranta, sanan mijinta shine babba. Kuma ta dau girman, domin har su Ummanah Yaya suke cemata, tana da yara guda biyar. Mai sunan Hajja ce babba, wacce yanzu take aure a Abuja, da yaranta guda biyu, yanzu gaba daya gida ance da ita, Yayar Abuja. Sai kuma Yaya Amira wacce ke aure a Zaria, ɗanta guda daya ne. Shekarar da ta ƙare ne, a ka aurar dasu, su hudu a cikin gidan. Daga ita Sai Mus’ab, shine babba a maza a ɓangarensu, sai kuma mai binsa Mai sunan kakanmu. Daga shi Sai Ummi dake auta a bangarensu. Sai kuma ‘ya’yan Mami guda shida, su kam ba’a gidan Galadima suke ba, kuma basa amfani da sunan Galadima kamar yadda mukeyi. A tsarin wanan gidan, yadda mahaifanmu ke amfani da Galadima haka muma mukeyi, kwata-kwata bama amfani da sunan iyayen mu, yadda mahaifina ke amfanu da Yunusa Galadima, haka nake amfani da Salma Galadima. Kuma kowa na cikin gidan haka yake amfani dashi. Legends pen. (08165383931 / 08129553971). *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* بسم الله الرحمن الرحي SHAFI NA BIYU (P.02). Mu hudu ne wajen Mahafinmu, Yaya Asma’u ce babba. Wacce tana cikin ‘yan matan da aka aurar shekara da ta kare. Sai kuma Muhammadu dake bin ta, sai ni sai Mai sunan Hajja. Wacce itace autar mu muna ce mata Iki. Itama Ummah bata gidan Galadima, amma kuma yaranta maza uku, duka a gidan Galadima suke, sai matan ne a wajenta, wa’yanda sune ƙanana dan muma nun girmesu. Aliyu, shu’aibu sai Kuma mai sunan Galadima. Sai kuma ɓangaren Alhaji ƙarami, shi ‘ya’ya uku gareshi, Yaya Khadija ce babba. Itama tana cikin wa’yan da aka aurar shekarar da ta ƙare, daman uku ne a cikin gidan Galadima. Sai kuma ɗaya daga gidan Mama. Sadiya ce ke bin Yaya Khadija, Sai kuma ƙanwarta guda daya. A cikin jikoki 27 da Allah yabawa Hajja, sai Allah ya jarabce ta da son guda daya, fiye da sauran jikokin. Har ake tunanin ta mafi son shi a kan wasu yaran na ta. Mus’ab Galadima. Tun haihuwarsa take nuna masa muguwar ƙauna, fiye da tsammani. Dan ko sanda yana jariri yayi kuka, nan Hajja zata fara balbalin bala’i, Ƙarshe dai Maman ciki, ba tajira lokacin yaye yazo ba ta miƙawa Hajja abunta. A cinyar Hajja ya taso, ɗangata, ɗan lele, rigimamme, mara kuma jin magana, sabida gata da ya samu wajen Hajja, kowa bai kyale ba a lokacin ƙuruciyarsa, har da kawunansa wa’yanda basuyi aure ba lokacin. Haka rayuwa tai ta tafiya, har a kazo lokacin da muka diro duniya, mu uku ne a set ɗinmu. Sadiya ce babba, sai kuma Walidah, ni ce ƙarama cikinsu. Tun tasowa ta, nake mugun son Kakata Hajja. Ina ƙaunar Hajja sosai da sosai, itama ganin haka yasa take ƙaunata. Sa dai Mus’ab ba ya ƙaunata ko kaɗan. Haka rayuwa tai ta tafiya, har a kazo lokacin da muka diro duniya, mu uku ne a set ɗinmu. Sadiya ce babba, sai kuma Walidah, ni ce ƙarama cikinsu. Tun tasowa ta, nake mugun son Kakata Hajja. Ina ƙaunar Hajja sosai da sosai, itama ganin haka yasa take ƙaunata. Sa dai Mus’ab ba ya ƙaunata ko kaɗan. Da zarar nazo wajen Hajja, zai fara dukana, ni kuma Allah yasa mun taurin kai, kafiya, naci, da kuma rashin haƙuri. Shekaru d’ai-d’ai har goma ne tsakanin ni dashi, amma a wanan lokacin da nake da shekara uku, shi kuma yake da goma. Da zarar ya dake ni, ko ya buge ni, ko ya harare ni, kai ko kallon banza yayimun sai fa na rama. Wanan ramawar da nake itace abun da ta kara haifarwa da Mus’ab tsanata, ni kuma wanan tsanar tashi itace ta raini tawa. Mus’ab bashi da kunya, ko yayunsa maza ma yi musu yake. Wanan rashin haƙuri nawa, yawan faɗa da ƙarata da Mus’ab ke kaiwa Hajja. Shi yaja ta fara yi mun faɗa, har tana hanani zama a ɓangarenta, da nazo zata fara cewa.”Ni Salame, wanan halin rashin haƙuri naki ya fara isata na. Ke kenan bazaki zo ba, sai kin addabarmun yaro?.” Cikin kuka nake cewa. “Hajja shine yake duka na.” “Ke kuma da baki da kunya, shine sai ki rama ko?.” haka kullum muke fama da Hajja, har naji zuwa ɓangaren nata ya fara fita a kaina. Abinda na kwana, na tashi da sanin shi shine. Mus’ab yana masifar son ganin ya kai ƙarata, dan tu ina ‘yar mitsitsiya idan ya dakeni, nayi masa Allah ya isa, sai yazo ya ce. “Ya ganni a waje, ina yiwa wani Allah ya isa.” haka za’asani gaba, ai ta jibga kamar sabuwar jaka, nai ta kuka kamar marainiya. Irin wa’yannan abubuwan, sune suka taru suka haifar da muguwar ƙiyayyar Mus’ab a zuciyata. Ƙiyayya irin mai girman gaske, sanan da yanda yake yiwa kowa rashin kunya, yasa na ƙara jin haushin sa. Sai da Ummanah ma Allah ya jarabce ta da ƙaunar Mus’ab. Ƙauna ta gaske, bata taɓa ganin laifinsa duk abunda zaiyi, ko da kuwa ya dakeni, ko yayi mun sharri an dake ni. Haka zan zauna nai ta kuka, amma ko a jikinta. Kamar yanda na faɗa. “Gidan Galadima gidane na haɗin kai, ƙaunar juna.” gida ne da babu wani ware, kowa yana son kowa,sanan kowa yana da set na, sakwanin haihuwa. A bangaren rayuwa, gida ne na masu rufan asiri, ba zaka ce mana masu arziƙi ba. Amma duk wani ci, sha, suttura, wajen zama, wajen karatu, munfi ƙarfinsu. Muna rayuwa a nutse cike da tarbiya, kowa na ƙaunar kowa. A ɓangaren kyau kam. Duk cikin gidan Galadima babu wanda yakai yayata Asma’u kyau. Duk da ance tana kama dasu Yaya Khadija, amma kowa yasan tafi kowa kyau A cikin wanan gidan. To ni da ita muna ɗiban kammani, ko da baza’ace nike biye mata a kyau ba. Bazan huce ta uku ba a cikin gidan Galadima. A maza kam a bayyane take, Mus’ab Galadima yafi kowa kyau, dan har wani shigen kama yake da wanan jarumin na indiya. (Aditya Roy Kapur) kawai shi Mus’ab yafi Aditiya faffadar fuska, kasancewar ta Aditiya ‘yar tsurut ce. Amma ni bana ganin wanan, sabida girmam tsanar da nayi mishi. Nikam zance ban taɓa jin yakira sunana ko sau daya ba. Yoo mutumin ma da harkar arziƙi ba ta haɗa ku ba, ta ina zai kira sunanki?. A haka har mu kazo matakin gama firamare, zuwa sakandire. Mukam a gidan mu ba’a cewa mace ba zatayi karatu ba. Sabida iyeyenmu nan duk da iliminsu, sai dai kuma ba’a taɓa samun wacce taje gaba sakandire ba, domin da zarar sunje matakin siniya samari zasu fara ɓulɓulowa kamar ruwa. Hajja kam cewa take. “Tun da samarin nan sunzo, to aurar da yaran nan, sabida lokaci daya mazaje ki zu war wa mace, da zarar sun kare to tsiyayewa zasuyi kamar hawaye.” Hakan ce ta faru kuwa, da zarar ‘yan matan gidan mu sunkai senior, zakiji anyi musu baiko. Suna kammalawa za’ayi bikinsu, wasu mazajen na barin su su ci gaba, wasu kuma basa ci gaba. Auren da’akayi shekarar da ta gabata, shine aure na uku da akayi, sabida idan aka tashi sai a hade mutum biyar, ko uku, maza da mata. A yanzu mukam mun shiga Ss1. Mu uku abun mu, sanan an saka ran aurar damu tare dasu Mus’ab, da wata buduruwarsa Junaidiya. Yarinyar kamar tsinken sigari haka take, ni ina mamakin yadda Mus’ab yake son yarinyar nan, duk kudinshi, duk gayunshi, duk ajinshi. Sai kuma wani lokacin nace, menene nawa?. A zuwa yanzu, tsanar Mus’ab ta danne ƙaunar da na kewa Hajja. Dan ko ɓangarenta banni xuwa, indai Mus’ab na garin. A kwanakin baya nai ta biyewa Mus’ab, ina zaginsa da masa rashin kunya, shi kam sai ya dakeni sosai, sanan yasa kawunnai na, ko yayumun su zaneni. Bansan mai yasa kaf ahalin Galadima, ake yarda da maganar Mus’ab ba, ni kuma ake kin yarda tawa. Ko dan shi yanayin magana cike da nutsuwa, niko da hayaniya nake magana. Sanan ina ƙaryatashi a gabansu. Haka za’aita jibgata kamar jaka. Akwai wataran da nayi niyar daukan fansa a kan Mus’ab, Naje har ɓangarensu lokacin Maman ciki na kitchen. Da sallama nashiga Kitchen tare da faɗin. “Maman ciki, aiki akeyi.” “Eyh, diyar ciki.” dariya nayi, sabida sunan da take kirana dashi kenan. “Ummi bata dawo ba kenan?.” “Ke wai lafiyanki, kike mun tambayoyi haka.” Murmushi nayi sanan nace.”Babu komai, sai anjima.” “Dawo mana, ɗiyar ciki.” Naji ta fada murya a sanyaye, alamun taji babu dadi. Haka kawai naji zuciyata ta karye, nafasa yin abinda ya kawo ni. Abinda ya faru kuma, jiya da daddare har yaja Yaya ilyasu ya mareni. Mun dawo daga makarantar magariba, sai wani dan ajinmu Walid ya tareni a lokon baya. Yana tambayata a kan buduruwarsa, wacce take ƙawata. Muna cikin magana, Mus’ab yazo wucewa, da sauri Walid yace. “Salma ga yayanki.” kallon Mus’ab nayi nace. “Naganshi, yayi kyau kamar rago.” gyaɗa kai yayi yahuce, kasancewar lokon da mutane. Shi kam bazaiyi abinda xai zubda mai da mutunci gaban mutane ba. Ina shigowa harabar gida, naganshi yafito daga bangaren Hajja. Da sauri na nufin ɓangaren nata, amma yarikemun hannu, juyowa nayi zan mai masifar da nasaba. Naji ya tsinkeni da mari. "Allah ya isa, Allah yagamaka da masifar duniya.” addu’ata ‘yar kullum gareshi, wacce shi kan shi ya haddace ta. “Zaki ci gidanku.” ya fada tare da jana ciki, ihu na fara kur mawa, ko Allah zaisa maman ciki tajiyo ni, amma Allah bai nufita ba. Kai tsaye inda Yaya Ilyasu yake yakaini. “Yayana, nagaji da abinda yarinyar nan keyi. Har ta kai ga abokaina sun fara mun magana a kan rashin kunyar da takeyiwa mutane a waje.” Da sauri na ɗago, tare da faɗin.”Wallahi karya yake, Mus’ab kai azzaulumi ne.” Yaya iliyasu ne ya tare ni da cewa. Legends pen. (08165383931/ 08129553971). *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* بسم الله الرحمن الرحي SHAFI NA UKU (P.03). “Tabbas kuwa, wanan ba rashin kunya bace. Salma mai yasa kike haka?.”Cike da jin haushi na sake buɗe baki nace. “Wallahi, karya yake min. Kawai ya tsaneni ne.” ban rufe baki ba naji, an ɗaukeni da mari. Tabbas marin ya shigeni, domin har wasu taurari nagani. Suna yawo a sama, daga nan ɗaki na huce. Ban san mene zanyiwa Mus’ab na huce wanan kayan haushin, sai dai kuma ɗaukar fansar duk kusanci dashi ne, nikam ina neman tsarin ubangiji da zuwa kusa dashi, ni ko a laira idan za’ayi mana Hisabi so nake tazarar mu ta kasance nisan sama da ƙasa. Idan kuwa har akace sai nuna gab da juna, ni mai iya yafeshi ce. Duk lokacin da Mus’ab, ya matso kusa dani wani irin turnuƙuƙi nakeji daga cikin zuciyata. Wani irin zafi kamar ana soyata. Idan nace na tsani Mus’ab, to na tsaneshi, bana fatan ko da rana daya naji na samu sasssuci daga tsanar da nayiwa Mus’ab. Yau ta kasance Lahadi, babu makarantar boko sai islamiyya. Muna zaune a compound muna wasa, har yanzu zuciyata cike da ɗacin marin da Yaya ilyasu yayimun jiya, kamar ance Salma fita waje haka naji zuciya na na fusgata. Kyawawan samari ne guda biyu, suna tsaye daga gefen gidanmu. Kyawawa ne sosai da sosai, cike da nutsuwa na fara tafiya zuwa inda suke, kamar wacce aka saka. ”Ƴan mata barka.” Daya cikinsu ya faɗa fuskarshi da murmushi. “Ina wuni.” na faɗa kasancewar sha-biyu ta kawo kai. “Lafiya ƙalau, dan Allah ko kin san gidan Alhaji idi me mai.” ɗaga kai nayi sanan nace. “Ai kuna kusa ma, gida na uku daga gidanmu.” “To inane gidan naku?.” ɗayan da baiyi magana ba tun dazu ya faɗa, cikin wata murya mai sanyi da zaƙi. “Kaji mazan arziƙi, ba irin su Mus’ab masu maganar mata ba.” na faɗa a raina, a fili kuma nayi murmushi na ce. “Wan can mai jan get ɗin shine namu, to daga na kusa da mu mai ƙofa, sai wancan mai ɓakin get na farko, to mai baƙin na biyu shine.” “Mungode Ƴan mata.” nayi murmushi, kamar an cemun juya idanuna suka faɗa cikin na Mus’ab, Ya harɗe hannye a ƙirjinsa yana kallonmu. Irin kallon da yakemun naji zuciyata ta buga da ƙarfi, da sauri nashiga gidansu Nana. Sai dai ko minti biyar banyi a gidan ba, iki tazo tace wai nazo inji kawu Mudi. “Innullahi, mai wanan mutumin yaje yace nayi kuma ni.” iki dai ba tace mun komai ba ta huce, na bita jikin a sanyaye. A tsakar gidan mu, na tarar dashi hannunsa rike da bulala ga Mus’ab can tsaye. “Kawu gani.” “Tsugunna ƙasa.” “Kawu mai nayi.” “Bazaki tsugunna ba.” ban kai ga tsugunnawar ba ya fara dukana, da iya ƙarfinsa, babu imani ko tausayi. Yana dukana yana faɗin. "Ke mara kunya mara tarbiyya ko, kina yin rashin kunya a gida ana kyaleki. Yanzu abun naki yakai harda fita waje, kiga mutane tsaye suna magana ki hau yimusu rashin kunya ko?.” zallan mamaki ne ya hanani cewa komai, wacce irin tsana Mus’ab yayi mini, mai nayi masa haka da zafi?, haka kawu mudi ya ci gaba da zabgamun bulal, har kuka shigo farkon labarin. *Cigaba* Nanata addu’a ta nakeyi.”Allah yagama Mus’ab da masifar duniya.” na jiyi sautin Walida, tashigo bangaren mu tana rusa kuka, Abinda ya fara zuwa raina shine. Mus’ab ya mutu, afili na furta. "Allah ka tabbatar.” shigowa tayi ɗakin mu tana faɗin. “Ummah, Yaya Mus’ab ne ya faɗi, ciwon kansa.” wani sanyi naji ya ratsa zuciyata, wanda kwata-kwata yau banji shi ba, tun bayan haɗuwata da wanan samari guda biyu. A gigice Ummanah ta fito, kamar wacce a ka ce mata, ni ko Yaya Asma’u sun faɗi. “Innullahi wainna illahir raji’un, Allah ka kawowa yaron nan saukin wanan ciwon kan.” Ummanah ta fada tana ficewa, da ido na bita ina taɓe baki. “Allah yasa har mutuwarsa.” na fada tare da kwanciya abuna, ban farka ba sai kiran sallar asuba. Tashi nayi na shiga toilet, na daura alwala nayi sallah. “Ummah ina kwana?.” Na fada daga inda nake, amma naji shiru. “Ina kwana.” still shiru, tashi nayi nafito falo tunda ita Ummanah na anan take zama lazimi, tun sallar asuba har bakwai. Rashin ganinta a falon yayi matukar razana ni, dakinta ta nashiga kai tsaye nan ma batanan. A kid’imi na fito xuwa b’angaren Abbanah, dakinshi na shiga na tarar dashi xaune da carbi hannunsa. Kallo ɗaya yayimun yasan da damuwa a tare dani. “Salma lafiya?.” “Abbanah, ina Umma?.” Murmushi yayi sanan yace. “Yayanku ne ba lafiya a asibiti suka kwana.” A jiyar zuciya na sauke, ni kam na ma manta da wani Mus’ab ba lafiya. Hanya na kama zanfita yace. “Ki hada musu breakfast, kuje ke da walida.” cuno baki nayi gaba, tare da ficewa. Kitchen na shiga na fara hada breakfast, cikin ƙanƙanin lokaci na soya doya da ƙwai, zuciya ta nayi mun tuƙuƙi. Nasan yadda Mus’ab ke mugun ƙaunar doya da ƙwai, domin ko a baya a ka kaiwa Hajja ba taci sai dai ta ajiye masa, har na zuba a plast sai kuma na tuna Mus’ab bai cin yamboll (Ƙosan doya), cikin hanzari na jawo doya nashiga ferayewa. A gaggauce na dadatsa ta na ɗora ta a kan gas, tare da balbala uwar wuta. Zuba doyar nayi a plast tare da tea na miƙawaya Abbabah, na ɗibi iya cikina, na ɗibawa Hajja sai kuma wani bangare na zuciyata ya rayamun kar na kaiwa Hajja, domin ita ke daure masa gindi. Amma fa inason Hajja ko ya ne, fita nayi zuwa ɓangarenta hannuna riƙe da doyar. Tana zaune jigom kamar wacce aka yiwa mutuwa, ina kyautata zaton jiya batayi bacci ba.”Ina kwana?.” na faɗa, ina shiga dakin. “Lafiya.” “Gashi.” na fada tare da miƙamata. “Babar taki ta dawo ne?.” girgixa kai nayi, sanan nace. “Nina soya.” “Menene kika soya?.” “Doya ne da ƙwai.” Murnushi tayi sanan tace. “Kin ɗibi na Asibiti.” a da kile nace. “Uhm.” daga haka na juya na fice. Ina zuwa na tarar doya ta tayi, aikuwa na sauke na fara dakawa, cikin ƙanƙanin lokaci na dake ta. Na yanka albasa da attatuhu na zuba a ciki, na kawo maggi da kuri na zuba a ciki, nasan baicin kifi hakan yasa na dakko kifin gwangwani na zuba a ciki, na hau mulmulawa. Cikin ƙanƙanin lokaci na mulmule ta tas, na kaɗa kwai na hau soyawa. Ina gama soyawa na juye a plast, nasan duk masifa yana shan ruwan zafi hakan yasa naki da fawa dasu. Zuba tea din nayi a kofi, na zuba doya da yamboll dina, na hauci. Sai dana ƙoshi, na hade ragowar doyar na juye a baƙar leda, na jefe a kwandon shara, zuciyata fari tas. Abbanah ne ya kirani ɗakinsa, bayan na zauna ya kalleni yace. “Salma, kije ki shirya kuje asibitinan yanzu.” “Abba wallah, ƙafata ciwo takemun sosai…” wani kallo da ya watsamun yasa na haɗiye yawon bakina, da ragowar maganar tas, na tashi na nufi daki, dogon hijabin Ummanah na dauka na zura, aikuwa yazo mun har ƙasa ina jaa. Ban ko damu ba, nashiga kicin na dakko plast din nasa a leda, a bakin ƙofar dakin na tsaya nace. “Kudin mota.” “Tasowa zanyi na kawo miki?.” a jiye ledar nayi, nashiga dakin ya bani dubu biyu, ba godi ba nagode na kadai na tafi, tunda dai bani na tambayeshi ba. Ɓangren su Walida na nufa, na sameta tsaye.”Mai kike jira?.” na tambayeta. “Lami nake jira ta gama abinci na tafi dashi; ina zaki ke?.” ta tambayeni , donin kowa zaiyi mamaki idan nace, Mus’ab zanje kai wa abinci. "Abba ne yasani girki, wai na kai asibiti, amma tunda ga wanan kawai kizo mutafi." na faɗa da biyu a raina, domin banason ya zamana abinda Ummi zata tafi dashi, Mus'ab ɗin nacin sa, anyi ba'ayi ba kenan. Ɗaki tashiga ta saka Hijabi itama, mu ka fice. A bakin titi mu kasami napep muka shiga, kasancewar kowa yasan asibitin da ake kai Mus'ab, ba ma shi kaɗai ba, kowa da kowa na gidan Galadima. A bakin asibitin mai napep ya sauke mu, naira duba daya na bashi ya ɗau ɗari biyar, yaban ɗari biyar. Muka rankaya cikin asibitin, har zuwa bakin ɗakin. A dai-dai na naja na tsaya, namiƙa wa Walida ledar nace."Shiga da'ita, idan kinfito ina bakin nan." "Haba salma, kishigo mana." "Wallahi walida ba zan shiga ba, ko da ace dubashi da xanyi, itace hanyar samun saukin shi da huri.” Ba tak’ara cewa komai ba, ta amshi ledar ta shige dakin ni kuma naja na tsaya, kamar wata mai gadi. Ina tsaye kusan mintina biyar, Ummanah ta leƙo sai ji nayi ance. "Sannu tabbatacciya." da sauri na juya, domin banma ji sanda aka buɗe ƙofar ba, da ruguwa zanyi a guje. "Ummah ina kwana." "Bansani ba, zaki shigo ko sai nazo nan na tsinke ki da mari." ta kowa na farayi a hankali, har zuwa bakin ƙofar ɗakin, a raina ina faɗin. "Lallai Walida da ni take zancen." Yana Kwance idanunsa na kallon ƙofa, aikuwa cikin rashin sa'a muka haɗa ido, aikuwa na murguɗa masa baki, tare da maka mai harara, game da yi masa gwalo a lokaci guda. Karo na farko a rayuwarsa da yaga nayi abu ya burgeshi, a cikin zuciyarsa yaji hakan. "Maman ciki ina kwana." "Lafiya ƙalau ɗiyar waje." kamar kullum dai dariyar mukayi, na matsa kusa da walida ko zama ban ƙarasa yi ba na maka mata mintsine tare da faɗin."Wallahi kinyi da ni." da sauri tace. "Wallahi bani na ce kinzo ba, Yaya Mus'ab ne." "Wallahi Walida ƙarya kike, aina yasan nazo." "To nima bansani ba, daga Mama ta tambayeni ya mutan gidan, nace lafiya. Sai ta ƙara cewa ke ya kike, nace ke kikayi girkin ma, shine Ummah ta ce mai yasa baki biyoni ba, ni kuma nayi shiru. Sai ji nayi yace tare kuke, na girgixa kai amma yace wai tare muke Ummah ta duba." Hararar ta nayi na ce. "Ni ban yarda ba." Ƴan minti na kaɗan na miƙe tare da cewa. "Zamu tafi." dai-dai lokacin shikuma ya buɗe baki ya ce. " Abinci..." Wani murmushi nayi tare da zama, Ummanah kuwa ta sakko tana faɗin. "Walida kun manta da tea." "Wallahi umma ba ni nayi komai ba, ko ledar ma sai a bakin ɗakin nan ta bani na riƙe." "Ai shikenan, Ummanah ta faɗa tana kwance ledar. Legends pen. (08165383931/08129553971). Daga page 10 zamu gama free pages, mu shiga paid pages, ₦500 kacal ne sai kuma masu buƙatar complete ₦1000. Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* SHAFI NA HUƊU (P.04). بسم الله الرحمن الرحيم "Wallahi umma bani nayi komai ba, ko ledar ma sai a bakin ɗakin nan ta bani na riƙe." "Ai shikenan, Ummanah ta faɗa tana kwance ledar. Bude idanu tayi, ganin yamboll kuma ta tabbatar wanan din aiki na ne, domin kowa ya kwana ya tashi da sanin cewa. Mus'ab bai cin yamboll. "Yunwa na keji." Mus'ab ya fada, wata dariyar mugunta ta tawomun wacce da kyar na iya tsaida ta, har sai da shi kanshi yaga alamun ina dariya. "Salma, mene kikayi haka, kinsan baya cin yamboll ko?." Hade rai nayi, sanan na ce. "Ummah shi ka dai ne damu." "Eyh shi dake ba da doya akeyi ba ko?." "A'a Ummah, yafi sauƙi ne." "Ke zanci gidanku wallahi, a gama dafa doyar azo a daka shine zakice yafi sauƙi?." "Wai menene?." Maman ciki ta tambaya, "Yamboll ta yo." Ummanah ta ba ta amsa, " Ai shikenan mu bari mu ci, ku kuma ku fita ku nemo mana tea, da kayan madara." Tashi nayi na amshi kudin, walida ta biyo ni har mun kai bakin kofa, Ummanah ta ce. "Saura ki siyo ruwan sanyi." Dariya nayi na fice, Mus'ab kam zuciyarsa kamar ta fito waje, ji yake kamar ya makeni da duka. Mun siyo kayan shayin mun dawo cikin asibitin naji ana cewa."Ƴan mata." kamar nasan murya, amma duk da haka naki tsaya wa, duba da yanayin yawan mutanen dake wajen bai zama lallai ni din ake kira ba. "Ƴan mata, bakya jina wai." a ka sake fada kusa dani, da alama mutumin yazo inda muke. A hankali na waigo idanuna suka sauka a kansa, daya cikin matasan da suka zo layin mu jiya, suka tambayi Gidan Alhaji idi me mai. Wanda baiyi magana sosai ba, ina tuna lokacin da yace. "To ina ne gidan naku?." Murmushi nayi masa sanan nace."Ina yini." shima murmushin yayi, cikin zazzakar muryarsa yace. "Lafiya kalau ƙanwata; me kikeyi anan?." "Ɗan-uwan mu ne ba lafiya, aka kwantar dashi anan." "Ayyah, Allah sarki muje na duba shi." Wani irin abu naji a zuciyata, amma kuma baxan iya masa musu ba, hakan yasa na ce. "Toh muje." jerawa mu kayi muka fara tafiya, Walida ta shige gaba mu kuma muna baya, duk naji nayi wanan fiyau. Ya cika wajen baki daya, a raina na ce. "Idan wanan yace yana so na, wallahi sai nayi sadaka, sabida yana da kyau, gashi ɗan gayu, mai aji, murya mai zaƙi. Nipa an gama tashin kai na." A haka muka ƙara so daƙin, walida ce ta ce. "Bari na sanar da su." gyada kai yayi, ni kuma naji ni a ta kure. Ban yarda da abinda Walida za ta ce ba, hakan yasa na ce. "Bari na bi ta." "A'ah ki jira mana." kallonshi nayi, idanuna sunyi wani kala na ce. "Ban san me za ta ce ba." "Mai kike tsoro to?." "Za fa ta iya ce musu, Saurayina ko wani abu." Murmushi yayi, sanan ya ce. "To menene a ciki, ko ki na da wani saurayin ne?." ƙasa nayi da kai na, ba tare da na ce komai ba. Shi kuma ya ƙara cewa. "Ko akwai ne." girgixa kai kawai nayi, dai-dai lokacin da Walida ta fito. Sai a lokacin na fahimci cewa, kofar bata yin ƙara idan a ka bude ta, shine yasa dazo banji lokacin da ummanah ta buɗe ba. "Ku shigo." ta faɗa, ni kam kamar munafuka haka na zama. Idanunsa a rufe yana kallon sili muka shigo, Maman ciki ce ta. "Ga waje mana basai ka xauna a ƙasa ba." "A'a Mama bari na zauna anan; ina kwana, ya mai jikin." "Lafiya ƙalau, mai jiki da sauƙi." su ka amsa tare. "Allah ya ƙara lafiya." "Amin, Mus'ab ga baƙo fa." Mama ta faɗa, a hankali ya buɗe idonsa ya sauke su akan mu, kasancewar ya tsugunna kusa da inda nake zaune. Kallo daya ya gane fuskar gayen, wa'yanda yaganni dasu jiya, tasowa gayen yayi zuwa idan gadon yake, tare da mi ƙawa Mus'ab hannu sukayi Musabaha."Ya ƙarfin jikin?." "Alhamdulillah." Mus'ab ya fada a da ƙile. "To Allah yaƙara afuwa." "Amin." "Zan huce, Allah yakara lafiya." "Amin-Amin, an gode." Su Umma suka fada, shi kuma ya nufi ƙofa. Walida ce tayi magana da ƙarfi yanda kowa zaiji."Salma kije ki raka shi mana." kamar mara laka haka na tashi, ina raba idanu nayi waje. A bakin ƙofa na tarar dashi. "Salma..." ya faɗi sunan, tare da ja cikin wani irin salo mai dadi. Sai naji kamar shi kadai ya iya kiran sunana. "Zan tafi, ngde da kulawa. Sunana Masrur, sanan wanan asibitin na mahaifina ne, kuma yana karkashin kulawata saboda haka, an dauke muku komai." "Mun gode, amma da ka barshi dan wallahi ban san ta yadda zan fadawa iyayena haka ba." "Salma..." ya ƙara kiran sunan na, a nutse na ɗago na kalleshi. "Ina sonki." Kara ɗagowa nayi na kalleshi, idanunsa suna kaina, da sauri nayi kasa da nawa a raina na ce."nima ina sonka." amma afili kuwa shiru nayi na kasa cewa ko uffan."Bazan ta kureki ba, zanbaki lokaci kiyi tunani. Ga lambata nan." ya faɗa yana miƙomin wani kati, hannu nasa na amsa sanan nace. "Nagode." ka ɗa kai yayi ya tafi, ni kuma na koma ciki. Kamar wata ɓarauniyar da tayi sata aka kamata haka na shiga cikin ɗakin. Sai dai duk cikinsu babu wacce tace da ni ko uffan, hakan yasa nayi matuƙar damuwa. A hankali na ce."Umma, mai walida ta ce muku?." banza Umma tayi dani kamar ba taji ni ba, kuma nasan taji, hakan yasa na koma ga Mama. "Mama mai walida ta ce?." "Mai kikaji wani yace miki?." Na girgiza kai na ce."Bakomai." "To kuma, ko kinyi wani abun ne?." na girgiza kai kawai, can 'yan mintina na ce. "Walida ta so mu tafi." ba ta kai ga magana ba likita ya shigo ɗakin. Bayan sun gaisa yace da su Ummah. "Ban san wane likita ke duba Mus'ab ba, kuma ko ma wane akwai matsalal da ba daga likitan mu take ba, dagashi yaron ku take." "Matsala kuma likita?." Mama da Ummanah suka tambaya, har wani hade baki sukeyi. Ni kam a raina na ce. "Allah yasa matsalal mutuwa ce." maganar likitan ce tasa na dago na kalleshi. "Eyh matsala, domin gaskiyyya ba aina hin ciwon dake damunshi ake fada ba, kuma da masaniyar sa domin ko magungunan da ake bashi, na asalin ciwon sa ne. Kunga kuwa sun hada baki da likitan suna ɓoye muku. Wani daɗi naji a raina, domin nasan babban ciwon ne kadai ake boyewa iyaye ba'aso su ji sabida kadan hankalinsu ya tashi. "To yanzu likita wane ciwo ne, na gaskiyya dan Allah." Ummanah ta fada kaman zatayi kuka, wani ƙululun abu ya tsayamun a ma ƙoshi yanda matarnan ta damu da Mus'ab ko ni bata damu dani ba, ji yanda take magana kaman zatayi kuka. Abban ciki ne yayi sallama, tare da Kawu mudi da kuma Yaya ilyasu. Shigowa sukayi baki dayansu, nida walida muka koma can gefe muka basu basu waje, kasancewar dakin babbane. "Kai ka sa tsohuwar mutane cikin damuwa." Yaya ilyasu ya faɗa. Likitane ya ci gaba da cewa."Kamar yanda na fada muku, matsalal shi ba ciwon kai bane kwata-kwata." da sauri Abban ciki yace. "To menene?." "Matsala shi a ciki take." "To amma mai yasa duk bayanan ku na baya yake nuna kai." "A'ah ranka yadaɗe, ko a file na asibiti cike ne, sanan magungunan da yake sha ma na ciwon ciki ne, kawai su na ambatar kai ne domin ɓoye muku." Ina daga gefe na fara addu'ar, Allah yasa afendes ne yanda za'a yanka shi karshe a ce ya mutu. "To yanzu likiti menene cutar?." Abban ciki ya ƙara tambaya, Likitan ne ya fara duba takardun hannusa, nikam hankali na kanshi. " I need you to stay calm, please. Cutar tashi ba wata babba bace, amma kuma lokutan da ta dauka a jikinshi ta kara girma. "Doctor, kana firgita mu Menene matsala?" Legends pen. (08165383931/ 08129553971). Daga page 10 zamu gama free pages, mu shiga paid pages, ₦500 kacal ne sai kuma masu buƙatar complete ₦1000. Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* SHAFI NA BIYAR (P.05). بسم الله الرحمن الرحيم " I need you to stay calm, please. Cutar tashi ba wata babba ba ce, amma kuma lokutan da ta dauka a jikinshi ta kara girma. "Doctor, kana firgita mu Menene matsala?" " He have been diagnosed with a rare condition called Hypersexual Hormonal Disorder HHD. It means His body produces an unusual level of sex hormones beyond control. That’s why kake yawan jin wani irin zafi, idan kana ciwon cikin. Kuma irin wannan sha'awar ba irin wacce ake iya da ƙilewa ba ce,da ƙile ta da yayi na kwanakin baya yasa ta zama babba har haka." "Wannan wace irin cuta ce haka, nifa bangane komai ba?." Mama ta tambaya cike da ruɗani. "Nima dai." Ummanah ma ta faɗa. Yaya Ilayasu ne, ya kallemu ni da Walida yace."Ku fita." Sim sim sim kamar munafukai muka fice, ni dai burina a ce mutuwa zaiyi. Bayan munfita ne likitan ya kalli su Mama yace. "Yana fama da wata irin cuta mai suna Hypersexual Hormonal Disorder. (HHD). Ma'ana jikinsa yana fitar da wani nau'in sinadarin sha'awa fiye da kima. Wanan ne dalilin da yasa yakw yawan jin wani irin zafi, da kuma wata sha'awa mai ƙarfi wacce har ta kan iya kayarda shi ƙasa." "Inullahi wa'inna illahir rajiun." su Mama suka shiga maimaitawa, likitan yakara da cewa."Tun farko bai bari anyi dogon bincike ba, a kan rashin lafiyar tashi, gashi har abun ya zama worst haka, ko kunyar ku yake ji oho." "To amma fisabillillahi, ko da yanajin kunyar mu bashi da 'yan uwa maza. Kawai sabida rashin kula da lafiya." Ummanah ta fada cike da damuwa. "To yanzu likita menene ai nayin maganin cutar?." Abban ciki ya tanbayeshi. "There’s no drug-based cure yet. But in most studied cases, emotional stability and natural intimacy especially within marriage. help the body regulate the hormones over time. Auren na iya zama magani a gareshi." "Shikenan likita, insha Allahu za'ayi." Abban ciki ya faɗa, likitan yakara da cewa."Yanzu za'a rubuta mishi drugs da zai na amfani dashi, zasu taimaka sosai da sosai." "To mungode." Ummanah ta fada, likitan yasa kai ya fita, Mus'ab kam idonshi a kulle angama to na mai asiri yanzu kowa sai yasan halin da yake ciki. "Yanzu fa Mus'ab da ka mutu d Wanan ciwon, baka da maraba da wanda yakashe kansa, kasani kuwa." Maman ciki ta fada murya a sanyaye, Ummanah ta dora da cewa. "Mus'ab, a duniyar nan babu kamar iyaye, ba'a ɓoye musu komai domin kowacce mafita tana daga garesu, ka bar ganin mun girma har mun haifi kamarku, duk wata matsala idan tataso mana, idan har mijinmu bazai iya magance mana ba, to iyayen mu muke nufa da ita." Tashi Abban ciki yayi ya fice, domin yasan duk abinda zai iya fada, Maman ciki da Ummanah zasu faɗeshi. "Kuyi haƙuri..." ya faɗa cikin sanyin murya, Ummanah ce tace. "Dan Allah ko dan gaba ku kiyaye baki ɗayanku." "Tom insha Allahu." Yaya Ilyasu ya faɗa, sanan yace dasu Ummah. "Jiya masu neman auren Sadiya sun sake zuwa, a kace dasu sudawo yau." "Lallai ne, Sadiya lokaci yayi." Maman ciki ta fada, inda Yaya ilyasu yace. "Saura Walida da kuma Salma, su kam kamar ma ba za su kai candy ba." "Eyh kam, bazasu kai candy ba." Ummanah ta fada, Maman ciki tayi murmushi. Can sai ga Abban ciki ya shigo,rike da ledar magunguna. " Gashinan, suma sai kayi wasa da shan su." Maman ciki ta amsa ba tare da ta cw komai ba. "Ni zan koma gida, zan samu Hajja nayi mata bayani, Muji abinda zata ce." "Tom shikenan."Maman ciki ta fada, shikuma yasa kai ya fice. Muna zaune daga gefe ya fito, da sauri muka taso tare da cewa."Abba zamu tafi muma." "A'ah ku xauna mana, ko za kuyi musu wani aikin." "Ai Abba zamuyi girkin rana, sanan mu na da islamiya." na fada sabida ni hankali na, na kan na koma gida nayi sadakar alewa, zan kaɗeɗen saurayi kamar Masrur ya ce yana so na, shine sabida nice nafi kowa butulci ba xanyi sadaka ba. "Shikenan ." ya fada tare da fita, Walida ce ta koma daki tayi musu sallama, nikam bayan Abba nabi sabida tsoron karma ya tafi ya barmu. Muna ƙarasawa gida na sauka nayi ɓangaren mu, ban ƙarasa ba naji muryarshi na cewa. "Ki cewa Abbanki ya same ni ɓangaren Hajja." "Thom." na ce sanan na ci gaba da tafiya, shi kuma ya juya ga walida. "Kira mun sauran kawunnanki." itama "Tho." ta ce, ta tafi kiransu. Ina shiga na tarar da Abbanah ya gama shiryawa. "Abba mun dawo." "Toh sannu da dawowa, ya jikin na sa?." "ya warke." na faɗa a gajar ce, sai kuma na ƙara ce wa. "Abban ciki, ya ce ka same shi ɓangaren Hajja." "Ya dawo?." "Eyh, shine ya dawo da mu." "Okay." daga haka ya fice, ni kuma nayi cikin ɗaki. A ɓangaren Hajja kam, gaba ɗayansu ne zaune sun sa Hajja a gaba da kallo. "Ni wai lafiyan ku?, kun haɗu kuma kun bini da idanu." Hajja ta faɗa, sai kuma ta ce. "ko dai Mus'abu ne ya mutu?." "A'ah Hajja, ba mutuwa yayi ba amma akwai matsala." "Tsarin ubangiji muke nema a kan kowacce matsala." Hajja ta faɗa, Abbanah kuma ya ce. "Yanzu Salma ke ce mun ya warke." "Eyh hakane, su za su ga kamar ya warke. Amma a bayanin da likita ya yi mana, ya ce ba cutar ciwon kai ba ce ke damun Mus'ab tun farko, ya ɓoye mana ne." "Waye ya ɓoye mana?." Abbanah ya faɗa cike da fushi, dan shi a tunaninshi likitan ne yanzu ya je suyi ɗauki ba daɗi, dan duk gidan Galadima babu wanda ya kai Abbanah fushi, da zafin zuciya. "Shi Mus'ab ɗin." "Innullahi wa inna illahr rajiun, yanzu wace cuta ce haka zata kashemun jika na, ɗan lele nah?." "Mus'ab, na fama da wata cuta wai ita Hypersexual Hormonal Disorder. (HHD). Ma'ana dai jikinsa ya na fitar da wani nau'in sinadarin sha'awa fiye da kima. Shi ke haifar masa da wanan ciwon cikin." Kuka Hajja ta saki tare da faɗin."Nashiga uku na, shiyasa nake ce wa yaron nan cike ke masa ciwo ba kai, sabida idan ciwon yayi zafi ciki ya ke riƙewa ba kai ba. Amma ya ce wai A'ah, yanzu idan ciwon ya kashe shi ina yake so na sa ka kaina." "Kiyi haƙuri Hajja." kawu Mudi ya faɗa. Abban ciki ya ɗora da cewa. "A yanzu likita ya ce hanyar samun sauƙi guda ɗaya ce, ayi masa aure." Abbanah ne ya ce. "Abinda ke raina kenan, dama ai akwai yarinyar da ya ke nema ko?." gyaɗa kai Abban ciki ya yi, sanan ya ce. "Amma ya na da kyau idan anje neman auren a sanar da iyayen komai." "Salan su hana shi, to wallahi ba da yawo na ba." Hajja ta faɗa. "Yaya ba fa cewa sukayi ya na da Mentel disorder ba, kuma ba cewa su kayi ya na sa yawan buƙata ba. Dan haka wanan ai ba matsala ba ne." Abbanah ya faɗa, Hajja ta cafeshi da ce wa."shine dai, yanzu ina so ku tashi daga nan kuyi gidan iyayenta a ba su komai da komai harda sadaki." "Shikenan, amma ni ai babu ni za'a je ko?." Abban ciki ya faɗa da alamun tambaya ga Hajja. "Uhmmm." ta faɗa a gajarce, sai kuma ya ƙara cewa. "Su ma masu neman auren Sadiya fa?" "Naga dangin Mahaifiyar ta ne, ɗan gidan Yayar Mahaifiyarta uwa ɗaya uba ɗaya. Ba najin sun cancanci a hana su, duba da Mahaifinsa kowa yasan shi, tarbiyar gidansu ba ɓoyayye ya baci." Abbanah ya faɗa. "Sanan yaron yana zuwa nan sosai da sosai, haka mahaifiyarsa." Itama Hajja ta faɗa. "Shikenan, sai a ba su watanni. Amma kuna ganin za' a haɗe dana yaron nan." "A'ah kar ku fara, banason auren sa ya huce wata biyu fa." Hajja ta faɗa cike da damuwa. "Shikenan." kawai suka ce sanan suka fice, dole sai sunyi tasu shawarar a waje. Ina shiga cikin ɗakin mu, nayi ɓangaren Ummanah. Ƙasan kayanta na shiga du bawa, nasan nanne wajen ajiyar kuɗinta. Cikin sa' a na gano su, naira dubu daya na dauka na ƙara da ɗari biyar cikin canji mota na, na fita siyo alewa sadaka. Shagon bayan gidanmu na je, na siyo lolipop mai tsinke, har leda biyu a cewa ta "idan zaka gode wa Allah, ka gode ma sa da babban masaki sai ya ƙara ma ka da wanda ya fi wanan girma." Ina dawowa harabar gidan mu, na fara ƙwalawa yara kira ina faɗin."Sadaka, sadaka." cikin ƙan ƙanin lokaci yara su ka fara ta ruwa cikin gidan mu. Daga na cikin gida har na waje, ni kuwa faɗi nake. "Duk wanda ya karɓa ya ce Allah yabar ƙauna." ai kuwa da sun amsa za kiji suna cewa. "An gode, Allah ya bar ƙauna." na cafe da. "Amin." abuna, zuciyata shar, Allah ya bani zankaɗeɗen saurayi da ga sama. Walida ce ta fito wajen da na ke sadakar, ta kalli ne ta ce. "Sadakar mecece haka kuma?." Jin wani yaro ya ce. "Allah ya bar ƙauna, yasa ta bi ni da idanu, ni kuwa na murje na ce. "Menene a ciki?." "Ce wa yayi yana sonki?." ta tambaye ni. "Ba ke uwar munafukai ba, a faɗa miki kije ki ya ɗa mutum." "Ya za'ayi na ya ɗa ki?." "Walida da ban san halinki ba." na faɗa ina ci gaba da sadaka ta. "Wallahi ba zan fada ba." "To ce wa yayi ya na so na, har da ba ni lambarsa." na faɗa hankali kwance. "Lallai ne, ki na cikin Alheri. Kin san Sadiya ma an ba da ita?." "Naji ƙishin-ƙishin dai." Na faɗa, ni dai hankali na na kan 'yan sadaka. Ganin kamar ta ji babu daɗi ya sa na ce. "Yanzu ke ma sai ki yi wa, Haidar magana kawai a kwashe mu." "kina ganin Haidar zai yi aure yanzu?." ta tambayeni cike da damuwa. "Mai zai hana shi tun da ya na sonki, ko ma ba za yi ba menene a ciki. Sai ki bawa wasu dama." "Ni kam na fi sonshi." "Sai ki zauna ki jirashi, ni dai wallahi ko yanzu a ka ce za'a ɗaurawa Masrur ne bin shi zanyi, na zauna na yi uban me a gidan?." Na faɗa ina murguɗa baki, kamar gaban iyayen nawa nake. Ƙarar tsayawar Napep ya samu ɗagowa tare, Su Ummah mu ka gani. Wani irin abun naji tsurum a zuciyatah, ga uban ledar alewa a hannuna, ga yara sun zangaye ni su na faɗin."Allah ya bar ƙauna." Legends pen. (08165383931/ 08129553971). Daga page 10 zamu gama free pages, mu shiga paid pages, ₦500 kacal ne sai kuma masu buƙatar complete ₦1000. Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* SHAFI NA SHIDA (P.06). بسم الله الرحمن الرحيم Ƙarar tsayawar Napep ya samu ɗagowa tare, Su Ummah mu ka ga ni. Wani irin abun naji tsurum a zuciyatah, ga uban ledar alewa a hannuna, ga yara sun zagaye ni, su na faɗin."Allah ya bar ƙauna." Sakkowa su ka fara yi daga cikin Napep ɗin, idanu na suka sauka a kan sa, a raina na furta. "Ya dawo bai mutu ba." na ja tsakin da ya fito fili, har Walida ta kalle ni, sai kuma na sake ce wa. "Kai ka ɗai dai za ka ci tsiyarka, ni kam lokacin ta shi na daga gidan Galadima ya yi." "Sadakar me a ke yi kuma?." Umnanah ta tambaya, bayan sun ƙaraso inda muke tsaye. Buɗe baki nayi zan fara wa'in- wa'in yaron da yake gaba na ya ce. "An gode, Allah ya bar ƙauna." da sauri nayi ƙasa da kai na, ban san da wane ido ne zan kalli Ummanah ba, Maman ciki kam ce wa tayi."Ƙaunar wa?." Shiru mu kayi nida Walida, nasan dai Walida ganin ina wajen yasa ba ta faɗi komai ba, amma da ba na wajen tuni ta shai da musu. Ummanah ce ta ce."Ku shigo da kayan." sanan ta huce, Maman ciiki ma ta huce. Ido nasa na kalleshi, wata irin tsanarshi mai nauyi ta durga a ƙirjina, ni ke nan ba zanyi masa mugun fa ta ya kama shi ba, duk da haka ba zan gaji ba."Allah ka gama shi da masifar duniya da ta lahira." na sake faɗa ina daukan kayan. Ɓangaren Hajja suka nufa, mu kuma mu kayi bangarensu. A raina naji dadin dawowar Ummanah, ko ba komai zan ɗauki wayarta na kira Masrur. Ban daddara ba, na mai da lolipop ɗita jakar islamiya ta, a ce wa ta idan na fita nayi sadakar a bata, dan wallahi sai na nunawa Allah godiyata da yabani kyakyawan saurayin kamar Masrur. Ƙarfe ɗaya da rabi nayi shirin Islamiyya, bayan na ɗau jaka ta na fito falo na ce da Ummanah. "Na huce." tsaya ki mika wa Mus'ab doyar nan. Turɓune fuska nayi sanan na ce. " Na ma kara fa." "To sai kin kai, ko abinda ya fi makara kika yi. Wai ni Salma yaushe ne zaki dai na yi wa Mus'ab wanan ƙiyayyar ne?." "Au ni ce nake ƙinsa?." Na faɗa a raina, a fili kuma na ce. "Ni ba ƙinsa na ke ba, kawai ba na son kowacce kalal alaƙa ta haɗa ni da shi." "Sabida ba ɗan-uwanki ba ne ko me?." "Umma kawo na kai."Na faɗa domin son tsayar da waccan maganar. "Salma ba fa ke ce kika haife ni ba, kin san da haka?." shiru nayi, ni ba na son a ci gaba da maganar, domin har cikin rai na ba na son wani abu da ya shafi Mus'ab a rayuwata. Ina tsaye ta gama soyawa ta miƙo mun."Sa a plast ki miƙa mai." ban ce uffan ba, na ɗau plast ɗin na zuba. Ga ba daya na juye a plast din na kama hanya na fice, na fito daga ɓangarn mu zan nufi ɓangaren su na ga Sadiya ta dawo. Washe baki nayi da faɗin. "Ka ga amarya, shine kika kwashe ƙafa ki ka tafi, wato sai da a ka ce an basu shine ki ka dawo." Dariya tayi sanan ta ce. "Wallahi dazu Amina ta ce mun, Mal isah ya ce sai ya ɓallani, shine ki ka ga na kwaso ƙafa na dawo." Dariya nayi sanan na ce."Ba kunya ki ka tafi gidan su saurayi ki ka zauna." "Yoo kunyar wa zanji, ina shan zumar ƙauna." ta fada ta na fari da ido."Uhm bari na mika wanan ɓangaren Hajja, amma kafin nan tsaya ki amshi sadakar ki." na fada ina a jiye plast ɗin a ƙasa. "Sadakar me?." ta tambaya ne da mamaki. "Allah ya kawo mun masoyi, na kece rai ni." Na faɗa ina miƙa mata alewan."Ki ce mun kusa barin gidan Galadima." "Mun kusa fa." na fada ina hucewa, ita ma tayi bangarensu. A hankali nayi sallama, amma ba'a amsa ba hakan yasa na shigo ciki kai tsaye. "Yanzu Mus'ab da wanna ciwon ya kashe ka fa?." Naji muryar Hajja na faɗa. Ahankali na ji ya yi magana cikin sanyin muryarshi."Hajja ai ina shan magani, ba zai kashe ni ba." "A'a nidai Mus'ab, gwanda kawai ayi auren nan. Irin wanwn ciwon na ku, aure ne kadai mafita." Nan take kwakwalwata ta gano mun cutar da ke damunshi, kuma gashi ɗazu naji likita ya ce tayi Worst. "Chaɓ, irin su ne muke ji a Novel kenan? Wa'yanda matansu ke ramewa sabida yawan sha'awarsu." wata muguwar dariya ce ta tawo mun da ƙyar na iya tare ta, sabida tinawa buduruwar da zai aura nayi kamar tsinken sigari haka ta ke. "Sai dai ta koma tsinken kwa-kwa." na fada a fili, ina dariya ƙasa-ƙasa na shigo dakin. "Baki iya sallama ba." Hajja ta fada ta na hararata, nima hararar na mayar ma ta sanan na ce. "Kun can kuna hirar ku ai ba za ku ji ba." "Ke dalla me yasa baki da hankali." hararar na mayar kanshi, sanan na ce. "Ni ce ma kai." azabure ya ta so ya yo kai na xai da ke ni. Hajja tayi saurin riƙeshi, tare da fadin. "A'a Mus'ab na hana ka." Koma wa yayi ya zauna ya na haki. "Ai da ka dake ni, wallahi sai ka yi da nasani, domin yanzu Allah yakawo mun mai tsayamun, wallahi Mus'ab idan ka dake ni har kotu sai mun je." Na faɗa tare da ajiye plast ɗin na juya. "Lallai yarinyar nan tabbata ki ke ji, to wallahi zaki zo ki same ni." Hajja ta faɗa, shi kuma ya ce. "Da kin barni na ɓallata." "A'a Mus'ab, ka dai na wanan saurin hannun." Shiru yayi bai ƙara ce wa komai ba. Ni kam ina fita na kaɗa kai na yi makaranta abu na. A hanya nai ta yiwa yara sadaka, haka 'yan ajinmu. Duk wanda na bawa sai na ce ya ce."Allah ya bar ƙauna." Kasancewar Ajin mu ba daya dasu Walida ba, ya sa ban fiya tsaya su tafiya ba. Allah bashii dawowa ma, ita kam Halima ba ma islamiyar mu ɗaya ba, ita hadda ta ke yi. A haka na shigo cikin layinmu, zuciyata fes sai dai ƙara hango Musrur da nayi ya ƙarawa zuciyar ta wa haske, a nuste na ci gaba da tafiya har inda ya ke. Da mayalwacin murmushi a fuskar sa ya tare ni da faɗin."Sannu da dawowa ranki ya daɗe." Wani sanyi na ji da ya ce ranki ya daɗe. "Yawwa sannu, Yallaɓai." na faɗa sabida kar na ce ranka ya daɗe ya zama kamar na kwaikwaiye shi gwanda na zo da sabon salo abuna. "Uhm, i apprecite this name." "You deserve it." na mayar mai cikin harshen turanci nima, domin ban son ya ga gazawa ta, ta kowanne fanni, domin yasan bani ka ɗai nayi sa'ar samunshi ba, shima ya yi sa'ar samu na. "So how was the school." "Alhmadulilah Yallaɓai, how was your work." "Everything great, ya mai jiki." "Jiki gashi can ya na fama." Na faɗa, in i don't care, ban son ma ya sake mun maganarshi. "Tun ɗazu ina ta expecting kiranki." Murmushi nayi kafin na ce."Ina ta jiran Ummanah ta dawo da ga asibiti kafin na kira." "Ouh, bakya da waya!?." Ya fada da mamaki ƙarara a fuskarshi. Sai naji na zama wata kala, dama bance ba. "Yaka ma ta na sama miki." Da sauri na girgiza kai. "Abbanah duka ne zai yi, kaba ri with time za'azo lokacin da zaka bani." Murmushi ya yi sanan ya ce. "I'm so glad to have you in my life." Ƙasa na yi da kai na, sanan na ce."Same here." Kamar an ce Salma juya, idanu na suka sauka a kan shi, a raina na ce. "Ko uban me yake yi a nan, oho." "Fulani, wanan kamar mara lafiyan nan ko?." "Fulani.." na sake maimaita sunan, ya masifar yimun daɗi. Na ma manta da abinda ya tambaye ni. "ko ba shi ba ne?." ya sake tambayata. "Yeah, shine." Na faɗa. "Oh ya warke sosai, gida ɗaya kuke kenan?." "Uhm, family house ne." Na bashi amsa, ni ban son maganar wan can Mutumin. "But you look alike kamar blood brother na ki." da sauri na girgiza kai sanan na ce. "Godforbid, cousin brother ne." Dariya ya yi sanan ya ce."Mene na Godforbid ɗin?." "Ni kam, i really hate this Mus'ab, mahaukaci ne fa ɗa zu fa ce wa ya yi wai zai dake ni." nan da nan ya haɗe rai, sanan ya ce. "Du ka kuma?." Na ɗaga kai sanan na ce. "Ai bashi da hankali." "Da'alama faa." shima ya faɗa. "Yallaɓai bari na shiga gida, Ummanah na jira na." "Okay, Fulani take good care I love you." "I love you too." Na faɗa tare da juyawa da sauri, har na kusa shiga gida ya ce."Am, Fulani kar ki manta ki kirani faa." Daga kai kawai nayi na huce, Mus'ab na tsaye bakin gate nazo zan huce, sai da na kalleshi wata sabuwar tsanar ta sake dirga a raina, sanan na ce. "Allah ubangiji ba danni ba, ba dan Halina ba, ba dan laifuka na ba, ka gama Mus'ab da katuwar Masifa ko iya duniya ne, masifa wacce za ta azbtar da shi." Legends pen. (08165383931/ 08129553971). Daga page 10 zamu gama free pages, mu shiga paid pages, ₦500 kacal ne sai kuma masu buƙatar complete ₦1000. Ranar litinin zamu fara posting paid pages, posting kullum, za'a fara siyar da complt ma ranar litinin, zaku iya fara payemnt tun yanzu Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931 *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* SHAFI NA BAKWAI. (P.07).. Sanarwa! Ranar litinin zamu fara posting paid pages, posting kullum, za'a fara siyar da complt ma ranar litinin, zaku iya fara payemnt tun yanzu Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. بسم الله الرحمن الرحيم "I love you too." Na faɗa tare da juyawa da sauri, har na kusa shiga gida ya ce."Am, Fulani kar ki manta ki kirani faa." Daga kai kawai nayi na huce, Mus'ab na tsaye bakin gate nazo zan huce, sai da na kalleshi wata sabuwar tsanar ta sake dirga a raina, sanan na ce. "Allah ubangiji ba danni ba, ba dan Halina ba, ba dan laifuka na ba, ka gama Mus'ab da katuwar Masifa ko iya duniya ne, masifa wacce za ta azbtar da shi." "Ke wai baki san wanan masifar da like jawa Yaya Mus'ab ba, Mala'iku su na amsa da ce wa Walaki ba." Kallon Sadiya da ke zaune kan doguwar kujera a falon mu nayi sanan na ce. "Wallahi Sadiya ni dan ta tawa mai sauƙi ce, indai har Mus'ab zai shiga Masifar da nake masa fata." "A'ah, dan Allah ki rage wanan muguwar tsanar." "Wallahi Sadiya duk safiyar ubangiji, wata sabuwar tsanar Mus'ab ke huda zuciyata." "Allah ya kawo miki sauƙi."Banza nayi da ita, sanan na miƙi zuwa ɗakin Ummanah. Wayarta da ke jikim chaji a soket na je ɗauka, amma ƙwalam ba ta nan. "Nasan tana dakin Abbanah, bari na je na ce tabani zanyi karatu." Na faɗa a raina tare da fice wa. Ban kai ga ɗakin ba naji muryar Ummanah na ce wa. "To yanzu zuwa yaushe zaku jira su?." "Eyh, zamu jira su zuwa sati ko fi. Dole dai idan su ka gama shawararsu su nai me mu." "Nima amma Alhaji, ciwon yaron nan ya mugun damana, gani nake kamar zasu ɓata mana lokaci. Kasan Likitan yadda ya nuna, yana buƙatar aure cikin gaggawa fa." "Gaskiyya ne, ciwon nan na shi na buƙatar iyali kusa-kusan nan, Allah dai ya bamu yadda zamuyi." Abbanah ya faɗa, dai-dai lokacin da nayi sallama. Ummanh ca ta amsa da faɗin. "Salma shigo ma na." shigar nayi kaina a ƙasa, sanan na ce. "Ummanah ina son nayi karatun hadda, idan babu damuwa." "To ai wayar na ɗaki." "A'ah Umma, ba ta jikim soket." "Eyh, ba nan na ajiye ba. Ki duba gefen fulo." Tashi na yi a raina ina ce wa. "Ko mai yasa ban duba nan ba oho." wani ɓari da ga zuciyata ya ce. "Rabon kiji wanan maganar ta su." afili na furta. "Mene haɗi na da maganar." kasancewar babu mai ba ni amsa, ya sa nayi shiru na ci gaba da tafiya zuwa ɗakin mu. Wayar na gefen gadon, hakan yasa na ɗauka na fara loda lambar ta shi, wacce tsabar yawan dubawa yasa na hadda ce ta. Bugun farko ya ɗaga wayar, kamar ya san ni ce ya fara magana. "Fulani barka da dare." idan na ce banyi mamaki ba, kuma kusan ƙarya ne. Domin yadda ya kira sunan da ƙarfin gwiwarsa, irin yana da tabbacin ni ɗin ce."Ba ita ba ce." Na faɗa ina murmushi. "Haba Fulani, tun kafin ki kira zuciyata ke cemun Next call is your future wife." Murmushi nayi sanan na ce. "Yakake?." "Not good." ya bani amsa, a ɗan tsorace na ce. "What's going on." "Fulani I'm missing you, so badly." "Same here, Vida mia." "Oh what a sweet name, amma naji dadin sunan." kunya ta ka mani, na ce."Amma Fulani yafi daɗi." "No, wanan ma yayi daɗi i really appreciate it." "Thanks you." na fada, cikin ƙarewar magana. "Fulaninah." Sassanyar muryarshi ta sake faɗa. "Vida Mia." Nima na faɗa, cike da sabuwar soyaya, a raina ina cewa. "Ni kam na dace, a rayuwar soyayya, domin Masrur ko babu ci babu sha, zan zauna dashi ko dan kyakyawar fuskarsa. Duk da Walida ta ce wai rawar kai ce, amma nafishi kyau." "Fulani, ina da tarin tambayoyi." "Tambayoyi kuma?." Na faɗa kai tsaye. "Yeah Fulani, amma ba tambayoyi masu damuwa ba, na soyayya ne." Murmushi nayi sanan na ce. "Tom ina jinka." "Fulani mai kika fara ji ranar da kika ganni." Shiru nayi ina sauraron zuciyatah. A hankali na fara ce wa."Ina zaune a harabar gida, na ji kamar ana kirana a waje, na tashi na fito, idanuwa na suka sauka a kan ka. Kyakywar farar fuskar ka ce ta fara burgeni." sai kuma nayi shiru. "Ci gaba mana Fulaninah." "Shikenan." Na faɗa, shi kuma yayi dariya. "Ni kam Fulani idan na faɗamiki ranar da na fara ganinki za ki yi mamaki sosai." "Yaushe?." Na tambayeshi. "Fulani, wajen 3weeks back. Na gan ki ke da ƙawayenki, kun dawo daga school. Tun lokacin na fara bin ki, ina ganin ki." Murmushi nayi mai sauti sanan na ce."Kasan maganar da nayi da ku, sai da Mus'ab ya ja a ka dake ni." "Fulani, wai mai kika yiwa Mus'ab ne?." "Nima ban sani ba, kawai dai na san ya tsane ni, nima haka." "Amma ya kama ta ku daina haka, ba kya ganin yadda kuke kama ne." "Ni kam har abada ba zan so Mus'ab." "Nima bance ki so shi ba, amma ku fahimci juna." cike da jin haushi na ce."Ko da a kwai wani abu da fahimtar juna dashi za ta yi mun?." "Ɗan-uwan ki ne fa." "Dan Allah mu bar maganar shi haka." Na fada kamar zanyi kuka."Shikenan, yanzu tambaya ta gaba. Mutum nawa kika yi dating kafin ni?." Shiru nayi ina son tuna wa, sai kuma na ce."Wani yaro ne Hafiz, tun muna aji biyu a islamiya daga baya kuma mu ka rabu." "Faɗa kuka yi?." Ya tambaye ni. "A'a, kawai yau da gobe da kuma girma." "Okay, Wa kika fi so a ƙawayenki?." "Ai ni bani da ƙawaye da suka huce 'yan uwana, Walida da Sadiya." "Wacece wacca nagan ku tare a asibiti?." "Walida, na bashi amsa." "Okay, yanzu yi mun naki kafin na ciga ba." "A wacce unguwa kake?." tambayar da ta fara zuwa bakina ba tare da na shiryawa fitarta ta ba. "Gwari avenue." Na girgiza kai, alamun naji."Akwai wata?." ya tambayeni, na ce."Eyh, mai ya baka kwarin gwiwar zuwa layin mu." "Zuciyatah." Dariya nayi sanan na ce."Na gama." "Ina da wasu masu yawa, amma naga dare yayi." "Uhm." Na faɗa, sabida bana son wayar ta kare. "Ki kwanta, sai Allah ya tashe mu. Kisani ina matuƙar ƙaunarki." "Nima haka." Na faɗa tare da gyara kwanciyatah, fuska ta ɗauke da murmushi ya katse wayarshi. Haka na kwanta ina ta murmushi, kamar wata sabuwar kamun hauka. Washe gari.. Da sassafe na tashi, sabida ina son zuwa boko duk da ba wani abu ake mana ba, sabida muna Ss2 ne kuma anyi exam ɗin third term har angama. Boko dai ajin mu ɗaya da Sadiya, amma Walida ta na Science ne, ni da Sadiya Muna art. Ita sadiya ma commerce take, kawai wasu subject ɗin mukeyi tare. Ni dai na ce ba zan wahalal da kaina a kan Karatun boko ba, dan yanzu ba wani aiki a ke samu ba, gwanda na karanci har kar kasuwanci abu na. Zaune nake a cikin class, na ware gefe na zauna hirar mu da Vida mia nah ta na dawomun ina murmushi ni kadai abu na. Safiyya ce ƙanwar Samira wacce Mus'ab zau aura ta shigo ajin mu, wata muguwar dariya ce ta tawo mun, ganin ta na tafiya kamar cokali. To a haka ma tafi Samira ƙiba, ga mamaki naga ta na yo inda nake, kau da kai nayi daga saitin inda take tawo wa."Salma Galadima." ta faɗa, bayan ta ƙara so inda nake, cike da haɗe rai na ce. "Ya a ka yi?." murmushi tayi sanan ta ce. "Lafiya ƙalau, ai yanzu mun zama 'yan uwa." "kun dai zama 'yan uwa, ni mene alaka ta da ku, har da wanda zaku aura." "Ai ko ba komai ɗan uwanki ne ko." "Kinga Safiyya, tashi ki bani waje." Na faɗa a tsawa ce, saukar da murya tayi sanan ta ce."Kiyi haƙuri, tambayar ki na zo yi fa." "Me zaki tambayeni?." "Dan Allah Kifaɗamun gaskiyya, nasan ba kya ƙarya kuma ba za kiyi ba." kallonta nayi sanan na ce. "Wai me zan fada miki." "Nasan kin san Mus'ab su na soyayya da Samira, to amma tun farko ba wata soyayya ba ce ta a zo a gani, dan bai taɓayi ma ta maganar aure ba. Kawai dai soyayyar tasu ta bazo ne, kowa ya sani to kwatsam su Abbanku su ka zo da maganar aure, bayan su Babban mu sunyi shawarar ba shi, sai ga wani zance ya fito. Wai Mus'ab yana dauke da wata cuta, kuma duk macen da ya aura za ta sha wahala a kan wanan cutar tashi, dan Allah ki faɗamun gaskiyya, nasan ba zaki ɓoye ba, sanan kin san Yayata ba wani kiɓa gare ta ba, kuma wallahi ba xan taɓa cewa daga bakinki na ji ba, ko a gidanmu." Legends pen. (08165383931/ 08129553971). Daga page 10 zamu gama free pages, mu shiga paid pages, ₦500 kacal ne sai kuma masu buƙatar complete ₦1000. Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ SHAFI NA TAKWAS. (P.08). بسم الله الرحمن الرحيم "Nasan kin san Mus'ab su na soyayya da Samira, to amma tun farko ba wata soyayya ba ce ta a zo a gani, dan bai taɓayi ma ta maganar aure ba. Kawai dai soyayyar tasu ta bazo ne, kowa ya sani to kwatsam su Abbanku su ka zo da maganar aure, bayan su Babban mu sunyi shawarar ba shi, sai ga wani zance ya fito. Wai Mus'ab yana dauke da wata cuta, kuma duk macen da ya aura za ta sha wahala a kan wanan cutar tashi, dan Allah ki faɗamun gaskiyya, nasan ba zaki ɓoye ba, sanan kin san Yayata ba wani kiɓa gare ta ba, kuma wallahi ba xan taɓa cewa daga bakinki na ji ba, ko a gidanmu." Tsuru-Tsuru nayi da idano, tabbas nasan komai da ta faɗa gaskiyys ne, Amma idan na fad'a mene makoma ta, nayi munafunci, ko nayi taimako?. "Wallahi, Salma ba zan ta ɓa cewa a bakin ki naji ba." Wata nannauyar ajiyar zuciya na sauke, sanan na ce."Kin san bani da alak'a kyakyawa da Mus'ab, abubuwan shi ba su shafe ni ba, kuma ba na saka kaina, domin nasaka SAKATA na kulle duk wata ƙofa da za ta had'a wani abu tsakani na da abinda ya shafi Mus'ab." "Nasani, Amma ba zaki rasa sani wani abu a kai ba, bani zaki yiwa ba Salma, 'yar uwata da rayuwarta." Shiru nayi ina tunani a cikin zuciyata, mai zai sa na ɓoye gaskiyyar nan, mene ruwana da tonan asirinsa, idan ma na rufa mai aairi ban tsane shi ba, gwanda na to na masa asiri ko mutuwa ne ma yayi, karewa. "Duk abinda na fad'a miki, idan har kika fad'awa wani ni ce na fad'a miki. Ubangiji ya gama ki da Masifa a rayuwa." da sauri ta gyad'a kai sanan ta ce. "Na yarda wallahi, babu wanda zaiji ke ce kika fad'amun." "Eyh, tabbas Mus'ab na dauke da cutar da ni kaina ban ma san sunan ta ba. Amma ta danganci iyali, itace wacce ke sa mata su rame sosai. Yanzu shigowarki zaki ga ina dariya, ganin ki ne yasa na tuno yayarki shine nay dariya." Shiru tayi, ni kam sai a lokacin na tu na ɓaranɓaramar da niya, daman ni a kwai mugun surutu, da fad'i ba a tambayeka ba."Shikenan na gode, kuma insha Allahu babu wanda zai ji maganar nan da ga bakin ki ta fito." "Shikenan na gode." daga haka ta tashi ta fice, ni kuma na maida hankali kan abinda nake kafin ta shigo. Haka na zauna a jin sukuku, idan wani ɓangarena zuciyata ya nuna mum abinda nayi ba dai-dai ba ne, sai wani b'arin ya ce. "Kinyi d'in, shi dai-dai yake miki." Muna tashi daga makaranta mu ka yo gida, ni dai burinah naje nayi waya da Vida.mia nah, ya fi mun wanan zancen Mus'ab ɗin. Sai dai ina shiga ɗakin Ummanah ta aika ni ɓnagren sa, na kai mai Abinci. "Wai Ummah ke ce kike da haƙƙin ciyar da Mus'ab ne?." Wani banzan kallo ta watsa mun wanda ya sani ficewa, ni ban san me Mus'ab kewa Ummanah ba ta ke mugun son sa haka. Ɓangaren Hajja na fara zuwa, bakina ɗauke da Sallamah na shiga ɗakin na ta. Ciki-ciki ta amsa mun, ni kam bai dame ni ba. "Ya na nan?." "Waye?." ta tambayeni, kamar ba ta san wanda nake nema ba. "Mus'ab." na faɗa a daƙile. "Allah magani maƙoci maye ni uwar su Yunusa matar Galadima, wanan yarinyar baki yi ba wallahi." "Yana nan?." Na sake fada. "Yana ɓangaren uwarsa." Murgu ɗa baki nayi na huge, har na fita sai naji ban kyauta ba, Hajja fa ba ita ta kemun abinda Mus'ab ke mun ba, dawowa nayi na ajiye plast ɗin sanan na zo inda take na zauna."Hajja." na kira sunanta. "Na'am Uwatah." ta faɗa. "Hajja, kin ware mutum ɗaya cikin jikokin, kin nuna shi kaɗai kike so, kika damu da shi, kuma hakan kan haifar da tsana cikin zuri'ar ki." kallona tayi sanan ta ce. "Salame ai ni kin nuna mun ban isa da ke ba, kin nuna mun ke ware cikin jikokina, sabida kin dauki tsanar duniya kin ɗora a kan wanda kika kamar na damu da shi." ganin Hajja ba zata fahimci abinda na ke so ta fahimta ba, yasa na kwashe ƙafafuna nayi waje. Ji nake kamar kar na shiga ɓangaren nasu, sabida nasan Maman ciki ba ta nan, walida kuma ba ta dawo ba, har na kai bakin ƙofa wani ɓangarena na zuciyata yace da ni."Yanzu fa yunwa yake ji, kuma yana jiran abincin nan, ke baki da hankali zaki kai masa yaci yayi maganin yunwar, kinga fa kin taimakeshi kenan." Da sauri na ce."Allah kar kasa ko rana daya na zama mai taimako ga Mus'ab." ina fadin haka na canja hanya zuwa ɓangaren su Sadiya, a zauren su na ɓoye plast din kar a gani, nasan da zarar angani topa sai nai kai mai. Sadiya na zaune tsakar gida na shiga, washe baki nayi ganin wayar Anty a hannunta, a fili na ce. "Antyn ba ta nan?." "Yanzu ta je gidan Anty Nadra, wai ta kawo kayan kitchen." "Su amarya, ni ɗan a ramun minti ɗaya nayi waya." Na faɗa, ban jira cewarta ba na dau wayar, a zuwa yanzu na haddace lambar Masrur tas a kaina, kira na danna bayan na loda lambar. Kamar ko yashe bugu ɗaya ya ɗauka tare da faɗin."Fulani nah." Wani sanyi naji a raina, sanan na ƙara yardarwa raina Masrur soyayyar gaskiyya yake mun, domin dana kirashi yake gane nice. "Na'am Vida mia." "Fulani, yau nayi kewarki sosai." "Nima haka, na si kiranka da safe amma ban sami lokaci ba har na tafi makaranta." "Nima Fulani na tanadi morning messages ɗina, sai kuma na tuna wayar Ummanah ce." dariya nayi jin ya faɗi Ummanah kamar yadda nake faɗa."Me ya baki dariya haka?." ya tambayeni, murya cike da so da ƙauna, wanda ban san lokacin da na fara gane su ba. "Wai Ummanah, irin yadda nake faɗa." Dariyar yayi shima sanan ya ce. "To ba Ummnah ba ce." da sauri na ce. "Eyh, Ummanah ni kaɗai." "Wallahi ban yadda ba." ya faɗa kamar zaiyi kuka, dariya yabani, ai kuwa na shiga yin abata babu ko ƙaƙautawa, sai da na gama sanan ya ce. "Dariya kike mun ko?." shima dai kamar zaiyi kukan. "Ni kai ne ka ban dariyan." "To me nayi na baki dariya?." "Kana magana kaman za kayi kuka." "To ai kukan zan miki, tun da kina rabani da Ummanah." "Ni dai ba zan baka Ummanah ba gsky." na fada, kuka har cikin raina da gaske."Shekrar ki nawa?." Naji ya tambaye ni. "Sha takwas da wata ɗaya." dariya yayi sanan ya ce. "Menen wata ɗaya?, sha takwas kawai hajiya." "Hajiya kuma?." na tambayeshi."Eyh mana, Hajiyata, Fulanita." "Wai nikam suna nawa ne da ni?." "Dubu biyu." ya bani amsa, kamar yasan tambyar da zan masa kenan. "To faɗo su muji." "Tom ki shirya." "Na shirya ai." Na bashi amsa a matse. "Fulani." "Ɗaya." yayi dariya sanan ya ce. "Gimbiya." na c e. "Biyu." ya k'arayin dariya, sanan ya ce. "Mai gadon zinare." "Uku." "ki daina lissafawa." na ce. "Thom." "Habibiya, Hajiya, Uwar 'ya'yana, Matata, mai ɗaki na, abar ƙauna, wacce nake so." Dariyar da nayi ce ta tsayar dashi. "Mai ya baki dariya?." Shiru nayi sanan na ce. "Duka kuma wa'yanan nawa ne?." "Ai baki taaya na gama ba." bude baki nayi da niyar yin magana, naji sallamar Anty, sai a lokacin na tuna inda aka aiki ni, da sauri na ce."Kasan aike na akayi?." "Ta ina zan sani baki fad'an ba, ina zaki." "Wai Mus'ab a ka ce na kaiwa abinci, tun ɗazu." "Maza-maza tashi ki kai ma sa." Tashi nayi ina fad'in. "idan na dawo zan kira ka, ko a wayar Ummanah ne." Sanarwa! Ranar litinin zamu fara posting paid pages, posting kullum, za'a fara siyar da complt ma ranar litinin, zaku iya fara payemnt tun yanzu Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. ci gaba "Shikenan sai anjima, love you." A jiye wayar nayi tare da fitowa, kai tsaye nayi ɓangarensu. Da sallama na shiga ɓangaren na su, sanin Walida ba ta dawo ba, kuma tun safe Maman ciki ta fita yasa na nufi ɗakin na shi, yana zaune kan kujera yana faman lallatsa da laptop ɗin shi, daman kowa yasan Mus'ab da aiki da na'ura, domin ko aikin da ya ke yi na na'ura ne. Suna da babban kamfani, wanda suke aiki da na'ura mai kwakwalwa sanan ma aika cin farin kaya ne, na hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC. Ciki-ciki nayi sallama, yayi kamar bai ji ni ba, nima kuma ban sa ke maimaitawa ba. Ajiye plast ɗin abincin nayi tare da juyawa, sai dai kiran suna na da yayi yasa ni tsayawa, ba tare da juyowa ba."Ke Salame." bantaɓa jin ya faɗi suna na ba, idan an tambayeni ma zance ba lallai yasan sunan, ashe shima salamen yake cewa, sunan da na tsana. Ƙin amsawa nayi jin Salame ya ce, na ci gaba da tafiya. "Ba da ke nake ba." ya faɗa a fusace amma cikin sanyin murya. "Ai ba suna na Salame ba." Na faɗa, zuciyata namun wani tuƙwiƙi domin ko kalma ɗaya bana ƙaunar ta haɗani dashi. "Ke ya dama wanan, ɗauki tsintsiya ki sharemun ɗaki." a wane sukwane na juyo nayi mai wani kallon. "Kana shaye-shaye ne?." Ganin ina ta kallonsa, idanu na kamar sa faɗo ƙasa tsabagen harara ne yasa shi cewa. "Ba da ke nake ba, ko baza kiyi ba ne?." "Wallahil azeem ba zan ba." na faɗa a fili, kallo na yake cike da mamaki, rashin kunyar tawa har ta kai nan kenan?."A karo na ƙarshe, ki ɗau tsintsiya ki sharemun nan." "Mitcheww." naja wani dogon tsaki, tare da yin gaba. Sai dai ban kai ƙofa ba naji an riƙomun hannu, ina juyowa a ka ɗauke ni da mari, wanda nima banyi wani dogon tunani ba, na ɗauke shi da nawa marin. Sai ƙarar ya bada Tas! Tas Legends pen. (08165383931/ 08129553971). Daga page 10 zamu gama free pages, mu shiga paid pages, ₦500 kacal ne sai kuma masu buƙatar complete ₦1000. Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* SHAFI NA TARA (P.09). بسم الله الرحمن الرحيم "Mitcheww." na ja wani dogon tsaki, tare da yin gaba. Sai dai ban kai ƙofa ba na ji an riƙo mun hannu, ina juyowa a ka ɗauke ni da mari, wanda nima banyi wani dogon tunani ba, na ɗauke shi da nawa marin. Sai ƙarar ya bada Tas! Tas. Da mugun mamaki ya ɗago ya kalleni, ni kuwa sai haki nake kamar wata zakanya, banyi au ne ba kuwa naji ya kwarfeni da ƙafarsa na faɗi ƙasa Tim!, ai kuwa ya bini da duka. Ya fusa ta iya fusa ta, nima kuma na fusa ta iya fusa ta domin baki na bai mutu ba, faɗi na ke. "Shege, mugu, azzalumi, kuma wallahi zai ka ga gatana, wallahi sai munyi shari'a da kai." shi kuwa duka na ya ke amma da ƙafa, cikin sa'a na riƙe kafar ta sa, na gan tsara masa wani mugun cizo, kuma nak'i ci kawa har sai da na had'o da fata, da sauri ya janye k'afar tare da matsawa, nan take zuciyata ta ce mun. "Faɗan bai k'are ba." ai kuwa na tashi da mugum guda na ɗane bayan shi kamar wata biranya, na shiga gantsara masa cizo a wuya, shi kuwa faɗi ya ke. "Baki da hankali ne?, sauka a kai na." Salatin da Ummanah ta saki ne ya sa jiki na wani irin mutuwa, kirjina ya shiga bugawa da k'arfi-k'arfi. "Sannu 'yar biri." sai a lokacin na fara ƙoƙarin dirga ƙasa, idanunta suka kai kan ƙafarshi da ke fitar da jini, ga kuma shatun haƙorana a wuyansa. "Kashe shi zakiyi kenan." miri-miri nayi da idanu tare da fad'in. "Ina shigowa ya kifa mun mari." Ba ta ko kula ni ba ta shigo ɗakin tare da kama hannuna ta shiga jana a ƙasa, kamar kayan wanki. "Nashiga uku na lalace." kawai nake iya fad'a a raina domin nasan yau na bushe har hanjina. "Ummanah dan Allah kiyi haƙuri, wallahi shine ba shi da gaskiyya, wai sai na share masa d'aki daga na ce bazan share ba shine ya mare ni." Sai da na fad'a kuma, na tuna ɓaran-b'aramar da nayi, ni a rayuwata kwata-kwata ban iya ƙarya ba, komai gaskiyya nake fad'a kai na tsaye. "Shine kika fara gantsara masa cizo ko, ke ga mahaukaciya, karya ko?." "Wallahi Ummanah ba haka ba ne, mari na yayi." ban ƙarasa rufe baki ba, naji saukar mari tare da bulala, ina ihu ina kororoto amma Umma ƙara zanbad'a mun ta ke. Daman Ummanah kwata-kwata ba ta iya duka ba, duk lokacin da ta dake ni sai tayi mun rauni, shi yasa Abbanah yayi mun fad'a kan na kiyaye abinda zai ɓa ta ma ta rai, to lokacin da ta da ke ni ma na ƙarshe a kan Mus'ab ne, kai Mus'ab ya zama masifa a rayuwata. Tun ina kuka da bata haƙuri, har na yi shiru gaba ɗaya duk wani ƙarfina ya ƙare, sai da ta ga ji dan kan ta sanan ta kyale ni tare da fice wa, ta bar ni kwance ina kuka. Nayi kusan minti goma a zau ne, zuciyata na ta saka mun abubuwa kala-kala, ta ce mun "in je ina bu ga masa dutse a kai, sai dai ko mene ayi mun.", ta ce mun."In je in ƙa re mai tana di, zagi ta uwa ta uba" ko hakan zai kawo karshen zumuncin nan." abubuwa kala-kala, ƙarshe na yanke mafita guda d'aya na tarka ta na bar gidan baki daya, na je gidansu Masrur ko a 'yar aiki ya kai ni, daga baya mu yi aurenmu. A b'angaren Ummanah kam, ta na ga ma duka na ta nufi ɓagarensu Mus'ab, ya na zaune kan kujera ya rasa mai ke masa dadi, sallama tayi d'akin ya amsa. "Yanzu kai Mus'ab yarinya k'arama za ka tsaya har ta mare ka, ba ka b'abbalata." "Ummah kiyi hak'uri, bana son na dake ta nayi mata rauni." "Da ba ka ballataba, ai ko shi Abban na ku idan yazo ya ji abinda ta yi sai ya ɓallata, kuma ya na dawo zan faɗamai." "Ummah dan Allah kiyi hakuri, laifina ne da nasa ta sharar." "To wallahi daga yau, har zuwa ranar da zaka bar gidan nan ita zata ke maka sharar ɗakin, kuma ka ci abinci idan zaka ci." ta faɗa ta na ta shi, alamun shi ma ya ɓata ma ta rai,a tsakar gida su ka haɗu da Maman ciki, ganin yanda ran Ummanah ke haɗe Maman ciki ta ce."To mai kuma ya faru da 'ya'yan naki?." "Bari ke dai, lamarin Salma ya fara isa ta, yarinyar nan kullum rashin arziƙinta ƙara gaba ya ke." "Salma yarinya ce fa har yanzu, wai bakya tuna lokacin da aka haife ta ne?." wata harara Ummanah ta watsa Maman ciki, sanan ta ce."A'a ban haife ta ba, yawo nake da ita a ciki." "Allah yabaki haƙuri, yanzu ta na ina?." "Ta na can ta na jinyar jikinta." daga haka Ummanah ta huce, tabar Maman ciki da sakkaken baki, ɗaki ta nufa ta ajiye jakar ta tare da shiga bayi, sauri-sauri take ta fito tazo ɓangaren namu. Ni kam tun da na yanke shawarar barin gidan, na shiga haɗa kayana, bayan na cika akwatina sanan na jawo wata katuwar jaka na shiga zuba wasu kayan ciki, har da jaka da takalmi na. Bayan na gama na shiga d'akinta, inda take ajiye kudinta na nufa, naira dubu uku na dauka, sai kuma nayi tunanin dubu uku tayi mun yawa, nan da Gwari avenue baifi 2500, haka yasa na ajiye dari biyar na fito, ina kokarin janyo jaka da akwati na ta shigo, kallo na kawai tayi ba tare da ta ce."Ci kan ki ba." ta huce ciki, ni kam na ci gaba da jan kayana. Ina daf da bakin ƙofa naji an cafke ni, juyuwar da xanyi na ganta da wayar charger ta computer Abbanah, ba wata-wata ta hau zabga mun, ni kuma ina rusa ihu. Mamam ciki ta shigo da sauri ta na fad'in."Innullahi wainna illahir rajiun, Menene haka dan Allah?." "Barni na targad'a yarinyar nan, nayi mata rau ni." "Kiyi ma ta rau ni, sabida me, haba dan Allah." Nikam narkewa na ƙarayi a jikin Maman ciki, ina faɗin."Wallahi sai na bar gidannan ba za'a kasheni ba." "kiyi shiru ke kuma." Maman ciki ta faɗa, Ummanah kam ajiye bulal tayi tare da shigewa ɗakin, kallona Maman ciki tayi sanan ta ce. "Je ki mai da kayan, kuma kar ki sake irin wanan abun ko da wasa." "Wallahi Mama bazan ko ma ba, duka na zata ci gaba, ni kawai a bar ni." "Ki je ki mayar na faɗa mi ki." Maman ciki ta sake faɗa. "Wallahi ko kin mayar sai na dake ki, kuma har can ɓangaren zan zo." Kuka na fara, maman ciki ta ce. "To ai ba ɓangarena zan kai ki ba, muje." tunda ta ce haka, ɓangaren Hajja zata kai ni. Ai kuwa can ɗinne, Hajja na gani na haka ta fara sababi. "Amma wanan uwarta ki ba ta da hankali, to wallahi ahir ɗinta." Ni kam wata tsanar Mus'ab ce sabuwa ta sake fidda rashe a cikin zuciyata, a kan shi anyi mun dukan da ba'a taɓa kwatanta mun ba, an kira mahaifiyata sa mara hankali, duk a kan Mus'ab, kai Mus'ab ya zama tauraruwa mai wutsiya a inda nake." Maman ciki ce tai ta ba Hajja haƙuri, sai da ta ga tay shiru sanan ta ta shi ta tafi. "Tashi ki haɗa ruwan ɗumi." Hajja ta faɗa tana kallona, bayan fitar Maman ciki, ba musu na miƙe nayi Kitchen, a heater na ɗora ruwan ɗumin, sai da yayi sanan na sauke na shiga na watsa ruwa, naji daɗi sosai a jikina, na zo nabi lafiya kujera na kwanta, banko sassauta da tsinewa Mus'ab, har bacci ya ɗauke ni. Sai wajen la'asar sanan na tashi, zaune na ganshi kan ɗaya kujera dake kallon tawa, amma hankalinshi na kan wayarsa yana dannawa, inaga ma baisan ni ce kwance kan ɗaya kujerar ba, miƙewa nayi ina turu baki, ina hararshi ƙasa-ƙasa, Allah ya gani na tsani Mus'ab, bana ko ƙaunar ganinshi domin a yanzu na fuskanci Mus'ab so yake ya rabani da Ummanah, domin a kwanciyar nan ta wa na ƙara tabbatar da hakan, indai nasamu saɓani da Ummanah tofa a kan lamarin Mus'ab ne, ko mene ribarsa oho, wani ɓari na zuciyata ya ce. "Mutumin da baya sonki, mene ribarsa idan bai rabaki da iyayenki ba?." a fili na furta. "Kurwata kur, mai ɗa ya ci ɗanshi mara ɗa ya ci ƙoƙon tsuliyarshi." Wani kallo ya watsamun, sanan ya ci gaba da danna wayarsa, nima na mayar mai da kallon da hausawa suke cewa. "Harara a duhu." tun da bai san inayi ba. Bayi na shiga na ɗaura alwala, na fito na ta da sallah, har na kamalla yana zaune, yana danna waya."Mai bautar waya." na faɗa a raina, tare da shiga ɗakin da Hajja ke ciki. "Hajja abinci." Na faɗa daga tsaye. "Ke fa matsalata dake rashin kunya da rashin mutunci, haka ake yi a gidanku." na cuno baki gaba sanan na ce. "Ke kuma matsalal ki mita da sababi." "Nayi mita nayi sababin, na rantse yanzu zaki ficemum a ɓangare." Shiru nayi nasan zata aika, kaddam ne daga aikin Hajja."To yanzu Hajja mai zan ci?." "Shiga kitchen, ki dafa taliyar yara ina da ita lodi-lodi." Kicin ɗin na nufa, na shiga haɗa indomie na, ina mamakin yadda Hajja ke cin indomie, a yanzu haka akwai sama da katan biyar a cikin kicin ɗin, ina tsaye har ta kamalla, na juye a faranti na dawo falon, yana nan zaune kaman mutun-mutumi, yana faman bautar waya. Bayan na ajiye na shiga ɗaki, nayi narai-narai da fuska na ce. "Hajja tawa." Baki buɗe take bina da kallo, kamar ta ga sabuwat hallita. "Hajjana, dan Allah wayarki zaki bani, na kira malamin mu na sanarshi bani da lafiya ya sa banzo ba." ita Hajja ba ta wami damu da waya ba, kuma kullum wayarta cike da katin waya, haka su Sadiya za su zo da Walida suyi ta ɗauka suna kiran samarinsu, ni kam bantaɓa ba sai yau, ko da yake yanzu na fara soyayyar. Dawo falon nayi, sabida naji ana cewa."Waya sa saurayi kana cin ainci tafi tsargawa." Nan da nan na danna masa kira kamar ko yaushe, sai dai yau kiran na shiga ya katse, kafin na gama tantance mai ya faru naga kiranshi ya shigo, murmushi nayi tare da kai lomar indomie baki na, bayan na ɗaga kiran."Fulani mai lambobi da yawa." Ya faɗa bayan na ɗaga."Mijin Fulani, mai gane Fulani a ko yaushe." Na faɗa cikin wani irin salon magana, dani ban ma san na iya ba, ko dan Mus'ab na nanne? Oho mun. "Fulani, yau kuma wayar wa aka samu?." Ya tambaya cike da kulawa kamar ko yaushe."Wayar Hajja ta ce." Na bashi amsa cikin cool voice, wanda ni dai ban san lokacin da na iya ba."Uhm, Ummanki, Hajjanki, to ni wai wa za'abani?." "Salma Galadima mana, ita za su baka, ni dai kabarmun Hajjana, da Ummanah." "Ai kam na barsu, tun da zasu bani abinda nafi ƙauna." Dariya nayi na ce."Zasu baka mana, mussaman Ummanah." "Yau mai Fulani ke ce?." Dariya na ƙarayi, sanan na ce. "Indomie ɗin Hajja na dafa." "Yau kina ɓangaren Hajja ne?." "Can zan kwana, ƙilama na dawo nan." "Kai Fulani, ai Umma ba za taji daɗi ba." "Uhm, zataji mana. Ai yanzu munafukai sun shiga tsakanina da ita." Dariya yayi, har ana jiyo sautin shi sosai ta waje, sanan ya ce."Fulani munafukai kuma." "Uhm, munfukai masu bacci da ido ɗaya." Na faɗa ina ƙara kai indomie bakina, gaskiyya na yarda waya da saurayi ana cin abinci tafi tsargawa."Su waye haka to?." ya tambayeni. "Na ce maka masu bacci da ido ɗaya." "Su ba su da suna?." "Uhm..." "La'ila ha ilallahu muhammadu rasulillahi, amma Salame baki da mutunci, Mus'ab ɗin na zaune kika saka taliyar yaran gaba kika cinye, shi dayake kawo wa baki zuba masa ba." Muryar Hajja ta tare ni daga niyar bawa Masrur amsa, dariya yayi ta cikin wayar tare da ce wa. "Fulani sai anjima." ban iya bashi amsa ba ya kashe wayarsa, sakamakon wani abu da yatsayamun a maƙoshi yaki tafiya, jin wai Mus'ab ke kawo wa Hajja indomie ɗin da nake ci yanzu, yau nice naci abinda Mus'ab ya kawo. Da wani mugun sauri na tashi na nufi banɗaki, domin kwararar da indomie din da naci, amma ina ciki na yariƙe ta katamau, duk yunƙuri na amai yaƙi fita, a dole na wanke bakina na koma ɗakin, ina ta faman cika da batsewa."Ke lafiyanki?." Hajja ta tambayeni. "Haba Hajja ai sai ki ce mun ga wanda ya kawo indomie ɗin, amma kika barni na ci haram." "Uwariyanki Salame, abincin ne haram?." "Habba Hajja, Haba Hajja ni dai baki kyauta mun ba." Sallama Babban ciki naji, sai kuma Abbanah ya na ta faman faɗa, ban ma iya ƙarasa tantance abinda yake faɗa ba, na tashi nayi ɗakin Hajja da nasan Ummanah ce ta faɗa masa abinda nayi ya zo ɓallani. "Har mu mutanen nan zasu mayar ƙananan mutane, har mu za'ayi wanan cin fuskar." Abbanah yake faɗa, shi dai Babban ciki yayi shiri ya zauna kan kujera, Alhaji ƙarami da kawu Madu ne suka shigo sai Yaya ilyasu, babu Abinda nake tamaimaitawa a raina sai. "Innullahi wa inna illahir rajiun, yau kashi na ya boshe. Duka wanan taron a kai na." "Lafiyanku wai?." Hajja ta tamabaya, bayan su gama zama. "Iyayen yarinyar da Mus'ab zai aura ne suka aiko, wai sun gano yana da wata cuta dan haka sun fasa bashi aurenta." Legends pen. (08165383931/ 08129553971). Daga gobe zamu gama free pages, mu shiga paid pages, ₦500 kacal ne sai kuma masu buƙatar complete ₦1000. Payment via. 8129553971 OpaY Sani Muhammad lawan. Shaidar biya. 08165383931. *SAKATA*❤️⚓️ 🌻Stroy and written🌻 By Sayyid writer (Legend)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* SHAFI NA GOMA (P.10). بسم الله الرحمن الرحيم "Har mu mutanen nan zasu mayar ƙananan mutane, har mu za'ayi wanan cin fuskar." Abbanah yake faɗa, shi dai Babban ciki yayi shiri ya zauna kan kujera, Alhaji ƙarami da kawu Madu ne suka shigo sai Yaya ilyasu, babu Abinda nake ta maimaita wa a raina sai. "Innullahi wa inna illahir rajiun, yau kashi na ya bushe. Duka wanan taron a kai na." "Lafiyan ku wai?." Hajja ta tamabaya, bayan su gama zama. "Iyayen yarinyar da Mus'ab zai aura ne suka aiko, wai sun gano yana da wata cuta dan haka sun fasa bashi aurenta." Wani irin dum! Naji a ƙirjina, a fili na furta"Na shiga uku." dan tsorona kar naji an faɗi sunana, ance ni na faɗa. "Shikenan sai sun kashe mun jikan, sai sun raba shi da duniyar, Mus'ab idan ka mutu ina zan sa kai na, ina zan sa rayuwata." Hajja ta faɗa tana matse ƙwalla, Abbanah ne ya ce."Hajja ki yi haƙuri dan Allah, iyayen yarinyar nan ba su kyauta ma na ba, kuma sun nuna su ƙananan mutane ne, amma zamu ɗau mataki a kan hakan." Abbanah ya ƙarashe maganar da alaman karaya, zuciya ta ce ta tsinke lokaci guda, ganin fuskar Abbanah da ta Hajja a haka, ga Abbanciki da Alhaji ƙarami sun zuba ta gumi, kawu Madu da Yaya ilyasu tsaye carko-carko,"Duk ni naja wanan abun." na faɗa a rai na. "Yanzu ya za'ayi kenan?." Hajja ta faɗa ta na ci gaba da kukan, Ummanah da Maman ciki sai Anty mamansu Walida ne suka shigo su ma, idanun Ummanah sunyi jawur, kamar ni a kace ba za'a ba wa Masrur ba, ina ga ma tayi kuka. Zama su ka yi su ma, Hajja ta sake maimaita abinda ta faɗa, cikin sharɓar hawaye. "Hajja zamu sake bashi zaɓi idan yana da wata, sai muje mu nema mai, idan babu sai aduba cikin 'yan Uwa." Abbanah ya faɗa, ni da ke cikin ɗaki na ce. "Sai dai ko can waje, ko ku bashi Walida da ke ƙanwarsa, tunda dai Sadiya an ba da ita, ni kuma ga Masrur abu na, daman ita ce soyayyarsu ke ƙasa na dabo." "Nikam Abba ba ni da wani zaɓi a yanzu." Mus'ab ya faɗa, wani kukan Hajja ta ƙara saki, sanan ta ce. "Shikenan, ya cire rai da auren. Ubangiji ka wadaran yarinyar nan da iyayenta." "Hajja kiyi haƙuri,amma ni ina da shawara." Ummanah ta faɗa."Kai Umma kin fiya shiga abinda ba ruwanki." na faɗa daga can inda nake a cikin rai na. "Wace shawara ce haka?." Hajja ta tambaya, zama Ummanah ta gyara sanan ta fara magana. "Mus'ab dai ɗan mune na gida, kuma tun da wanan maganar ta fara fita ta na zaga gidajejen wa'yanda a kaje nema masa aure, to haka za tai ta zagayawa, ƙarshe ko ina su hana bayan an gama tozarta shi." "Hakane wallahi, abinda yake ta faman sani kuka kenan." Hajja ta tare Ummanah, Abbanah kuma kallon ummanah ya yi sanan ya ce. "To mai kike gani?." Shiru ta yi na 'yan mintina, sanan ta sauke wata ajiyar zuciya. "Mai zai hana mu haɗa aurensa da Salma, tun da muna da ita a cikin gida, kun ga dai Sadiya har anyi mata bai ko, ita kam ina ga ko saurayi ma ba ta dashi." Ai ban san lokacin da nayi wani tsalle ta tagar Hajja na dirgo falon, sai gani kamar wacca aka jefo. "Wallahi Ummanah ina da saurayi, ina da wanda na ke so, ko Hajja za'a tambaya yanzun nan na gama waya dashi, a gaban ma shi Mus'ab ɗinne, dan Allah kar ku auran Mus'ab." Gaba ɗaya na rikice, na manta a gabansu wa nake, haka shima Mus'ab, ji yake ana magana kamar ihu, amma kwakwalarsa kam dai ta ɗauke, babu abinda yake nanatawa a ransa sai. "Ummah karki yi mun haka, bana son yarinyar nan, natsane ta, bana ko son ganinta." Abbanah ne ya da ka mun wata tsawa, wacca ta sani haɗiye maganar da nake shirin yi, amma jikina sai karkarwa yake, hawaye na bin kuncina, zuciyata na wanu irin tsalle kamar zata fito waje. "Amma Allah yayi miki albarka da wanan shwarar." Hajja ta faɗa ta na murmushi."Har mu za'ayi wa hulaƙanci, jikoki 27 Allah yabani, ba a isa a hulaƙantani kan ɗaya ba." Hajja ta sake faɗa, Abban ciki kam cewa ya yi. "Tabbas wanan shwarar tayi, sai dai yakama ta a duba ita yarinyar." "Har wani haƙƙi take dashi, da ya huce ta yi mana biyayya." Abbanah ya faɗa cike da ɓacin rai, dan shi maganar da Abban ciki yayi ma ta ɓata masa rai."A'a Yaya, a duba yarinyar nan." Alhaji ƙarami ya faɗa. "Yanzu idan ace yarinyar wajenka na nemi ayi wa haka, cewa zakayi a'a ko me?." Hajja ta faɗa kamar zata yi kuka."Ni Hajja ba haka nake nufi ba, kuma kin sani da Mus'ab da Salma da kowane yaro dake cikin gidanan, ɗaya nake ɗaukansu, bantaɓa banbanci su a kan komai ba, Sabida haka na taso naga yayuna sunayi, duk cikin mu wanda bai godewa Abban ciki da Abbah ba sai Allah ya saka musu, tun tasowar mu suke tsaye a kan mu, har zuwa kan yaranmu dan haka bana banbance tsakanin 'ya'yansu da nawa yaran, amma Hajja ki kalli yanda Salma ke yi, a bata damar idan wanda take dashi ɗin ya dace, sai a bawa Sadiya Mus'ab ɗin." "Ai har gwanda sadiyan." Mus'ab ya faɗa, bayan ya dawo daga suman da yake."Ni kam Alhaji ƙarami sai nake ganin kaman Salman ce ta fi cancanta, domin ita nata saurayin da take iƙirarin tana da shi, bai ko taɓa zuwa ya gaida ku, bare kuma mu Mata, sanan idan har Salma ba ta taimaki ɗan uwanta ba, wa zata taimaka?." Ummanah ta faɗa, shiru Alhaji ƙarami yayi, sai kuma a lokacin Kawu Madu ya ce."Tabbas hakan yayi, kuma wanan shine amfani da ranar zumunci da zaman lafiya, mu ɗin ahali ne guda, a kullum burin mahaifinmu mu zama tsintsiya ɗaya, gashi Allah ya amsar addu'arsa ta hanyar bamu mataye na gari, nima ina goyan bayan wanan abun." Maman ciki dai ba ta iya cewa komai ba, tabbas tana farin ciki da hakan, kuma ta ƙara yadda Ummanah macece ta gari, sai dai kuma tana tausayina, domin ta san ba na son Mus'ab kuma shima bai so na. "Yanzu zuwa yaushe za'asa ɗaurin auren?." Abban ciki yayi magana, wani irin ihu na saki tare da zubewa ƙasa, domin nasan tun da Abban ciki yayi na'am da maganar to fa sai dai wani hukunci na ubangiji fasa wanan auren. Shi kan shi Mus'ab ji yake kamar ya ƙwalla ihun, dan yana buƙatarsa sosai."A haɗe shi da na Sadiya wata biyu." Abbanah ya bashi amsa. "A'ah wallahi, tun da ita ta gida ce sati uku ko biyu ya isa, domin kusan ba lafiya ba ce dashi." Hajja ta faɗa."Hakane kam Hajja, ni a ganina kwana goma sha huɗun zaifi." Ummanah ta bawa Hajja amsa. "Shikenan, Allah ya nuna mana." Abban ciki ya faɗa, tare da tashi, haka kowa ya tashi sai a lokacin Maman ciki ta kula da cewar bana numfashi, da sauri tayo kaina tana faɗin. "Yarinyar nan fa ta suma." Dawowa su kayi kaina, banda iyayen mu maza da suka fice, Anty ce ta samu ruwa ta bawa Maman ciki ta shafa mun, can bayan 'yan mintuna na sauke ajiyar zuciya tare da buɗe ido, suka sauka a kan Ummanah, ai kuwa na tsala ihu tare da tashi zan fice, da sauri suka riƙeni har da ita Ummanah ɗin, turza ƙafa kawai nake bana iya magana. "Innullahi wa'ina illahir rajiun." kawai Hajja ke maimaitawa, kowa yayi shiru sai karatu da ake mun, tunaninsu Aljannu na tayar, nikam kawai zafin ƙiyayya ce, ta samun harda haushin Ummanah, domin zuciyata babu abinda take nuna mun sai, zallan tsanar da Ummanah tayi mun, gwada kawai na bar musu gidan, son da nake su daina karatun yasa na tsaya da abinda nakeyi, hakan yasa suma su ka tsaya. "Dan Allah kar ku auran Mus'ab, bana son shi, Ummanah mai yasa ko da yaushe kika zaɓi ki ba ƙanta mun." Saukar marin da naji a fuskata ya sa nasaki wani fitsari mai mugun zafi, da gudu na ƙara kwasa zan fice, Mamman ciki ta roƙoni. "Nutsu Salma, idan aka barki ina zakije da gudun." Shiru nayi ina kallon tare da zazzaro idanu, kamar wata karya. "Ku kyaleta da gidansu, yanzu zan saka a ɓaɓɓalamun ita wallahi." Hajja ta faɗa tana hararata. "Kuma wallahi Mus'ab ne, insha Allahu sai kin aure shi, kinyi biyayyar aure, kin haifa masa 'ya'ya, wanan rashin zama ƙarƙashin inuwa ɗayan naku, bi'izinillahi sai ya zama Alheri a rayuwar ahalin gidan Galadima." Wani mugun Haushin Hajja yazo ya dirja a ƙirjina, gaba ɗaya na rasa menene yake mun daɗi, kukan ko shirun?."Tashi muje." Umanah ta faɗa a tsawa ce, tashi nayi kamar mara laka a jikina, ji nai iska na ƙoƙarin dauka na tayi wurgi dani, dan gaba daya na koma 'yar tsurut. A waje muka ci karo da su Walida sun tawo da gudu, ban ko kallesu ba nayi ɓangarenmu, suka rufamun baya har zuwa cikin ɗaki. "Salma mai ya faru?, ance kin ta da Aljanu a ɗakin Hajja." ji nayi a zuciyata, daman Aljannun nayi ko na ƙarya ne, nayiwa Hajja mugun duka, amma mu tara lokaci na gaba."Wai muna tambayarki, kinyi shiru." "Ku tashi ku kyaleta, mugun hali take ji." Ummanah da ta shigo ta basu amsa, tashin su kayi suka fice, na haɗa kai da gwiwa tare da fashwewa da kuka mai ƙara ina faɗin. "Wallahi bazan auri Mus'ab ba, wallahi ko za'a kasheni da duka." ba ta ko kalleni ba ta ci gaba da abinda take, ni kuma na ƙara cewa. " Wallahi ko tsinemun ne sai dai ayi." A ɓangaren Mus'ab kam, Mama ce ta kalleshi, sanan ta ce. "Ka tashi mu huce ko kaima kukan zakayi?." bai ce uffan ba ya tashi yayi gaba, ai kuwa suna shiga ɓangaren su ya zube a ƙasa tare da faɗin. "Mama Wallahi ba zan auri yarinyar nan ba." Bai kai ga rufe baki ba, Mama ta ce. "Wallahi Mus'ab ko bayan babu raina, ka ƙi auren yarinyar nan, ko ka musguna mata bayan aure, ban ya fe maka ba." To jama'a, mun iso iyakar free pages, kuma daga nan zamu faɗa cikin labarin, cikin rigima da zallar ƙiyayya. Gashi dai ance za'ayi musu aure, shin Mus'ab zai bari ya auri yarinyar da bai so, ko Salma za ta auri namijin da tafi tsana?. Idan har anyi auren, yaya zaman zai kasance, ya Salma zatayi da soyayyar Masrur? sakata ce zallan kiyayya da dumin ƙaddara! Paid pages suna ɗauke da abubuwa masu matuƙar yawa, da ɗaure kai. N500 kacal. Masu buƙatar complt kuma 1k ne. 8129553971 Opay Sani Muhammad lawan. Shaidar biya ta nan 08129553971/ 08165383931. Paid pages zai fara zuwa ranar Monday, masu buƙatar complt 1k.