*Assalamu alaykum brothers and sisters I am back again with a romantic, secret and funny love story....* Hope you people will enjoy it💡 🔊🔊🔊SANARWA 🔊🔊🔊 Duk Wanda yasan idan ya karantamin littafi zai kalleni a matsayin yar iska kada ya sake ya karanta, idan kuma ya karanta ya zageni to gaskiya ban yafeba❌ *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM......* *INA MIKA GODIATA GA ALLAH SUBHANAHU WATA'ALA DAYA BANI IKON DAD'A KAWO MUKU WANNAN LITTAFI NAWA MAI SUNA* 🎀ŞΔ₣ŘΔŽ🎀 Ina rokon Allah daya bani ikon gamawa Lapia 🙏(ameen) ALLAH KAYI DADIN TSIRA GA MANZONKA ANNANBI MUHAMMAD (S, A, W) ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMAD, WA'ALA ALI MUHAMMAD, KAMA SALLLAITA ALA IBRAHEEM WA'ALA AHLI IBRAHEEM, INNAKAHAMIDUN MAJEED, RABBANA ATINA FIDDUNYA HASSNA WAFIL AKHIRATI HASSNA WAKINA AZABANNNARR 🙏🙏🙏🙏🙏🙏 🎀🎀 SAFRAZ 🎀🎀 Episode 1 *Written by oum aeyman*🖋 MADARASATUL TAHFEEZUL QUR'AN WA TARBIYATUL AULAD......... 🚶🏻‍♀Cikin makarantar na shiga, ban zarce ko inaba sai stairs, Hawa stairs d'in nayi zuwa azuzuwan dake sama. Ajin farko na kalla naga an rubuta kisa'i Auwal a Saman kofar Ajin, na biyu ma an rubuta kisa'i sani, na uku kisa'i salees....... Haka Dai nayita wuce azuzuwa Dayawa ko wanne da sunanshi a sama. Yawancin azuzuwan akwai malamai aciki Wanda babu kuma xakaji suna surutu sama-sama Saida nazo Ajin karshe sannan na tsaya. Cikin Ajin nakalla : gaba dayansu manyane, domin daga y'an sha takwas zuwa ishirin da uku za'a iya samu..... Abinda yafi bani mamaki shine sunfi kowane aji surutu...... Saman Ajin na kalla naga an rubuta "(IBN KHATHEER)" kubiyo bayana donjin labarin wadannan 'Daliban ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ Wani kyakkyawan saurayine Wanda shekarunshi baza su wuce ishirin da daya zuwa da biyu ba, zaune yake akan kujerar da'aka tanada Don zaman malamai ya d'ora 'kafa d'aya kan d'aya ya karkace hular dake kansa wadda daka kalla zaka gane mai tsadace...... "Wallahi malam Abdullahi (shugaban makarantar) ya rainamu kuma ya Raina mana wayau, yarasa malaman dazai ri'ka kawo mana sai 'yan 'kunanan yara?! Mufa ba yara bane anymore domin Kaf cikinmu babu under 18yrs🔞, kuma naga ko a United States d'an 18yrs yanada right ⚡balle a 9ja.... Sannan kuma dukanmu babu Wanda ba'a university yankeba...... ni abinma dayafi 'konamin rai shine maimakon ari'ka kawo mana malamai Maza sai a rika kawo mana mata, jifa wadda ta tafi ancemin ko shekara ishirin da uku dakyar in zatakai. Dad'a gyara zama yayi "to wallahi ni kuma inanan duk wadda aka kawo saina koreta daga ajinnan....... Raf raf raf 👏👏👏👏y'an Ajin sukad'au tafi, wani saurayine Wanda bazai wuce shekarun na farkonba ya mi'ke... "Wow gaskiya safraz ka birgeni sosai, kuma duka abubuwan daka fad'a gaskiyane, muma kuma bazamu ta'ba watsa maka 'kasa a idoba.... kuma komai zakayi we are behind you and we will always support you dude..... Mikewa daga kujerar safraz Yayi "badai yau akace za'a kawo mana Wata malamarba? To kabarni da ita kugani ko sati biyu baxatayiba zata gudu da kafarta... y'an ajinne suka dad'a d'aukar tafi 👏👏👏yey safraz Muna godia....... wani seat 💺 dake gefe ya karasa ya zauna, A'kidatul Islam ya bud'e yana karantawa.... his face look very innocent Kamar bashi bane tagama shakiyanci yanzuba. Abdul ne ya zauna a kusa dashi "abokina kana muraji'a ne? murmushi safraz Yayi eh Abdul, so nakeyi na haddaceta duka..... dariya Abdul yayi "abokina ga brain ga iskanci " tafawa sukayi 👋 sannan yaci gaba da karatun shi........ "Assalamu alaykum" Wata siririyar murya sukaji tayi sallama a Ajin Dasauri suka d'ago suna Kallonta, sanye take da dogon light blue d'in hijab har kasa sannan kuma fuskarta sanye da niqab. Idonta 👀ne kawai a Waje ta 'bulin niqab d'in... Atare suka Amsa "wa'alaikumussalam" gefen white board d'in dake manne a jikin bangon Ajin ta matsa "sunana NAWAZ MUHAMMAD" ni aka turo a matsayin wadda zata ri'ka yi muku QUR'AN da fiqhu . KUTUMAR UBAN CHANN.... cewar safraz, amma idan ka kalleshi zaka rantse bashi yaceba domin ya maze..... cewa tayi "waye yamana ashar a ajih? dukda y'an Ajin sunsan Wanda Yayi amma sai sukace "malama zagi kuma? gaskiya mudai bamujiba. shiru tayi sannan taci gaba "to yanzu inaso Kowa ya mike ya fad'a min sunanshi domin musan juna..... babu musu suka mimmike suka fad'a...... "to Alhamdulillah, yanzu wace sura kuke? had'a baki sukayi duka Abdul yace RUM fatima tace QASAS, zainab tace AL IMRAN , safraz yace ANKABUT, Osman yace BAQRAH...... cewa tayi "to to to ya Isa, kuna nufin Kowa surarshi daban? had'a baki sukayi Eh malama! Kujera taja ta zauna "to babu komai Insha Allah zaku sameni me hakuri da sau'kin Kai, Abu d'ayane banaso shine idan na koyawa mutum karatu yacemin be iyaba.... Sannan kuma inaso muhad'a kammu domin tsintsiya d'aya bata Shara.... cewa sukayi "to malama.... QUR'AN ta ciro a Jakarta ta bud'o suratul baqrah "Wanda yake a baqrah a wace aya yake? Usman yace aya ta 25 cewa tayi "OK karantawa tayi sau Hudu sannan tace" wanda yace ankabut a wace aya Yake? safraz ne yasha mur "aya ta 400, ido ta zaro, aya ta 400 fa Kace? cewa yayi Ayyah sorry malama Ina nufin aya Ta sha hudu... "cewa tayi worry not, sannan ta karantamai shima sau Hudu..... haka tayita binsu har saida ta karanta surori sha tara..... agogon hannunta Ta kalla 6:30pm ta gani, cewa tayi "time d'in tashi Yayi "sallu alal nabiyul Kareem! da sauri safraz yace malama Don Allah Inada tambaya kafin a tashi... "OK inajinka Menene? malama dama jiyane nayi mafarki yankeshi tayi "Ayyah saidai ban karanci fassarar mafarkiba! da sauri safraz yace malama ba Haka nake nufiba... cewa tayi to inaji 👂 karkace kanshi yayi gefe Kamar me shirin yin kuka sannan kuma duk Yayi squeezing din fuskarshi 🙎‍♂Kamar mai shirin yin kuka, "malama dama jiya da dare ne nayi mafarki wai na sadu da Mace kuma dama tashi daga barci sainaji wandona a ji'ke... dad'a mutstsike fuskar yayi Kamar ze rusa ihu ''shikenan malama yanzu nazama d'an wuta kenan tunda nayi zina koh? ha'ki'ka malama nawaz taji nauyin tambayar amma yanda taga fuskarshi dauke da tashin hankali sai ta daure tace " haba kada kayi kuka mana, ba zina kayiba domin abin a mafarki ya faru ba'a gaskeba, Abu d'aya nakeso ka gane yanzu shine ka zama baligi kuma an bud'e maka littafi domin yanzu duk abinda kayi za'a ri'ka rubutawa me kyau ko mara kyau.... dad'a 'bata fuska yayi "malama kina nufin babu komai kenan? "Eh babu komai wanka kawai zakayi Sai kacigaba da sallolinka, to malama kenan idan na koma gida inyi wanka da sabulu 🛀🧼.. cije lebenta tayi sannan tace "nifa wankan janaba nake nufi.. dad'a karkace kai yayi nifa malama ban iya wankan janababa shida omo akeyi ba sabuluba? aranta cewa tayi wannan wane irin bagidajene? "bada omo akeyiba da zallan ruwa akeyi me kyau Wanda Bai chanza daga kalaba ko danndano ko kamshi, maana dai tsarkakakke me tsarkakewa ... zaka karkata bokitin ruwan ka fara wanke hannu saika wanke Al'aurarka sannan kuma kayi alwala amma karka wanke kafa, saika wanke kanka sau uku kuma ka tabbatar ko wane gashi ya ji'ku da ruwa kuma kagaka ri'kayi kana chud'awa zaka iya fara wanke bangaren jikinka na dama sannan saika wanke na hagu, zakuma ka iya wanke Saman jikinka sannan kayi kasa kahada da kafafuwan ka wanke .... murmushi yayi to malama nagode ... addu'a sukayi sannan tace to sai gobenku! Ta fita daga Ajin cike dajin nauyin tambayar da safraz yayi mata, had'e kuma da mamakin irin halinshi na rashin jin kunyar kalamnshi... tana fita daga Ajin sukadau ihu yeeyyy Sai namu safraz...... kujerar data tashi yaja ya zauna "ya kukaga wannan salon? cewa sukayi wallahi yafi nada ma.... safraz yace ai tunda naga Kowa ya fad'i surarshi daban kuma naga bata damuba sannan kuma ta karanta daidai na fara tunanin mezanyi mata.... sai wannan tunanin ya fadomin, Amma PA ta bani tsoro domin naga ta Amsa hankali kwance..... kunsan meye "had'a baki sukayi A'a oga safraz " cewa yayi naso ta cire niqab d'in saboda Mufi gane yawan shekarunta domin nidai a yanayin muryarta nasan bazata wuce 17-zuwa-18 ba..... y'an Ajin sukace Eh wallahi... "murmushi safraz Yayi dukda haka kubarni da ita saina koreta duk hakurinta... Mikewa Yayi zuwa hanyar Waje sauran y'an Ajin sukabi bayanshi suna tafi duk fuskokinsu dauke da annuri..... Wata compressor blue black naga safraz ya bude driver seat ya zauna,, igniting dinta yayi sannan Yayi reverse yafita daga gate d'in makarantar ... y'an ajinsune keta d'aga mishi hannu suna cewa boss sai. 2MO shima d'aga musu hannu Yayi sannan ya Kara speed d'in motar,, d'an gaba kadan yaga malama nawaz tana tafiya a nutse, rage gudun motar yayi yanata binta a hankali....... kubiyoni donjin meyasa safraz yakebin malama nawaz, wai shin zai iya korartama kuwa.. kumama wai to waye safraz ne????????? ????? TAKU AKULLUM HAFSAT ALIYU SHUAIBU CHIKAJI WATO OUM AEYMAN..... 😎*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* 🤳by oum aeyman Episode 2 Binta yaketayi har suka shanye street d'in duka, layin dake dama tabi, shima yana biye da ita Amma Yayi d'an nesa da ita saboda kada tagane ana binta.. Gida na hudu ta shiga, babu laifi gidan yanada kyau domin duk Wanda yaga gidan yasan megidan irin masu kudin Da ne.... Murmushi safraz yayi ''Ashe gidansuma babu Nisa. Wani Murmushin ya kumayi "ai kuwa tunda tabari nasan gidansu ta shiga uku Dani... Wayarshi ya ciro a aljihu, security ya cire sannan ya shiga contacts, Wata number da'aka yi saving da "MY WORLD" yayi dialling... daga can bangaren naji ance "sweetheart yakake? Murmushi yayi "Ina Lapia mummy, dama nakirane na fada miki zankai Abdul gida saboda yau bezo da machine ba. "to sweetheart kayi sauri ka dawo saboda banaso dadyn ka ya dawo bakanan.... Cewa Yayi "to mum as u said Insha Allah....... Sannan ya yanke wayar... Masallacin dake d'an gaba kadan ya karasa domin gabatar da sallar magrib.... ✨✨✨✨✨✨✨ Ita kuwa malama nawaz tana shiga gida ta tarar da umma (uwargidan babanta) zaune a tsakar gida.. Risinawa tayi "Barka da yammah umma! Kamar abin arzi'ki umma tace Barka dai nawaz, har kin dawo daga gantalin? Itadai nawaz batace komaiba ta wuce d'aki, a zaune ta tarar da umminta a Kujera rike da hijab da alamu tana shirin yin sallah ne.... "Barka da yammah Ummi " "yauwa Nawaz Kin dawo? Ya makarantar? "Lapia ummi Amma gaskiya nidai dakyar in zancigaba da zuwa...... haba Nawaz bansanki da raki ba, ace yau d'aya daga fara zuwa harkin karaya? "ummi wallahi dalibanne Marasa kunya ga tambayar bala'i sannan kuma wai Kowa surarshi daban,.... haba Nawaz ace duk yanda nasanki da hakuri? ummi wallahi da Matsala..... Ummi tace "to yau adakinma bazaki cire Dan gadonba (niqab) Ace mutum shi kullum baza'a ga fuskarshi ba Kamar aljani.... cewa tayi "zan cire ummi, kwance igiyar niqab din yayi...... Wow godia ta tabbata ga Allah subhanahu Wata'ala daya yi wannan halittar 🤩 nikaina saida nashiga shakku Anya kuwa itace sanye da niqab? farace irin milky white dinnan Kamar (tamanna bathia) ga face dinta very well shaped Hancinta irin siririnnan ne kuma tsawonshi har kusa da cute lips d'in ta wanda suma light pink ne kuma da alamu batasa lipstick 💄 ba. idonta madaidaici me dauke da zarazaran eye lashes.. kwayar idonta bakace sosai, kasancewarta Fara Sai hakan ya Kara mata wani sirrin kyau.... tanada siririyar gira wadda ta kusa hadewa....... Mikewa tayi "ummi bari naje nayi alwala! "to " kawai ummi tace... tsakar gida ta fita, a inda tabar umma anan ta tarar da ita bata tashiba. fampoo Ta karasa ta Kunna Ta tara butar dake hannunta.... Harara umma tabita dashi "shegiya Sai kyau Kamar aljana Amma babu mashinshini... ace Mace har ta Kai shekara 25 Amma batada saurayine saboda tsabar ba'kin jini..... Itadai Nawaz batace komaiba domin inda sabo ta saba da maganganun umma. Amma abinda ya bani mamaki shine jin danayi umma tace shekarun nawaz 25 ... Anya kuwa gaskene? Saboda ayanda naga nawaz bazata wuce shekara 17 ba...... alwalarta ta gama Ta wuce zata shiga d'aki, "abbanku na dawowa Zansa Yayi Shela a masallaci inda me sonki saiya badake sadaka, cewar umma tana dada doka mata Wata uwar Harara.... d'aki ta shige donyin sallarta domin yanzu maganganun umma sun dena bata haushi saima Daria da suke bata........ tayi ruku'u a raka'a ta biyu kenan wani yaron makwaftansu ya d'aga labule, ummi yagani rike da chasbaha alamun tana azkar..... "ummi wai aunty Nawaz tazo inji wani mutum a Waje...... mamakine ya rufe ummi lokaci d'aya had'e da farin ciki, domin rabonda ashigo gidan nan ace ana sallama da nawaz shekara ta uku kenan..... cewa yaron tayi to yasir je Kace gatanan zuwa, fita yasir Yayi.... Nawaz na idar da sallah ta waigo fuskarnan Kamar ta zabga ihu "haba ummi Daga ance ana sallama Dani saikice ace ganinan, kumafa bakisan ko wayeba...... daka mata Tsawa ummi tayi "nace d'in, in kinada hukuncin daza kiyi min saikiyi koh! Baza ki tashi ki fitaba saina bata miki rai? niqab ta dauka a hannun Kujera a fakaice domin idan ummi tagani bazata barta ta fita dashiba..... still a tsakar gida ta tarar da umma Harara tabita dashi zuciyar ta na tukukin ba'kin ciki, wato duk abinda tayi ya karye kenan koh... Itadai Nawaz zaure Ta karasa ta saka niqab dinta..... Mutum ta gani tsaye ya juya baya a Gefen boglary d'in gidan... Karasawa tayi "Assalamu alayku........ kasa karasa sallamar tayi ganin Wanda bata ta'ba zatoba ko a mafarki......... bata rai tayi "meya kawoka gidanmu? MASU KARATU KUNSAN WA NAGANI👀❓ safraz na gani tsaye yana mata murmushi "malama wankan da kika koyaminne Sai Bayan naje gida kuma na manta..... aranta tace da alamu dai wannan yanada Tabin hankali. "to kuma ya akayi kasan gidan mu? Cewa Yayi "malama google na Duba " Mamaki abin tabata "Ta tabbata Tabbas wannan kwarkwar ne..... dad'a maimaitamai tayi sannan tace kayi sauri kaje kayi kasan salloli ne akanka da yawa....... Hannu yasa a aljihu ya ciro wata wayar daban "malama ga wannan ki rike a hannunki saboda koda naje gida idan na manta sai in kiraki ki tunanin...... Duba wayar tayi "iPhone" tace aranta. cewa Yayi malama don Allah ki Amsa... Amsa tayi tace to, yanzu kayi sauri kaje gida, kaga dare yayi. harta juya yace malama Don Allah babu Wata addu'a daxaki bani Don indena irin wannan mafarkin........ murmushi tayi "I guess aure kawai zakayi domin shine mafita.......... juyawa tayi, daidai nan umma dake labe a zaure tana lekensu ta shiga gida da gudu.... a tsakar gida ta tarar da umma, "Ashe yau kwarton naki be biyaki a hotel d'in dakike zuwa bane shine ya biyoki gida ya kawo miki...... Cewar umma da ranta keta tafarfasa saboda taso taji me suke cewa Amma batajiba kuma gashi taga ya bata wani abu kuma shima batasan meyeba..... 'Daki Nawaz ta shiga, bataga umminta a falour ba saidai ta shiga cikin d'aki, "Ummi ashema d'an ajinane, wai tambaya yazo yi,,, kinga harda bani wayarshi wai idan yaje gida koda ya manta zai kuma kirana ya tambayeni..... ummi tace abinda nake fad'a miki kenan Ke kuma kina biyewa rudin shedan... ki daure kici gaba da koyarwar Sai kiga Allah yayiwa abin Albarka. nawaz tace to umma...... atsakar gida naga umma ta kasa kunne a jikin kopar shiga nawaz tanaso taji mai suke cewa, amma kasan cewar suna ciki batajiba..... d'aki ta koma ta Kira fauziyya ('yarta) "hello fauziyya Dan Allah kizo gobe domin aikinmu ya karye.. d'aga chan bangaren fauziyya tace meya faru? umma tace nidai saikinzo sannan ta yanke wayar...... To masu karatu wai Ina safraz ne? Motarshi dayayi parking a wani lungu yashiga ya tuka zuwa gida Yana tafe yana murmushi domin yasan burinshi ya kusa cika na korarta..... Azuci yake magana "wai ita koda darema da niqab take yawo? kuma naso naga fuskarta...... Wani bangajejen mansion naga ya nufi gate d'in, babu Wanda yazo budemai Amma sai naga gate d'in Yana zugewa da kanshi.... gidan yakai plot bakwai domin a gefe swimming pool ne harda foot ball field, dasu flowers iri iri chan wajen karshen gidan na hango gymnasium da garden a gefe.... Ko parking mai kyau beyiba ya fito daga motar, wani Babban apartment ya nufa da sauri, yana Isa gurin kopar ya zuge yashiga ciki. Wata hamshakiyar hajiya na gani zaune taci uban Ado Kamar wadda zata gasar kyawawa ... Shekarun ta bazasuwuce irin arbain ba zuwa da d'aya... jikinta safraz ya fad'a "mummy wallahi yau nagaji " Murmushi tayi "sweetheart ai kaine idan nace kabari driver yakaika saikace kai kafi karfi.... kawar da maganar yayi dacewa "bari Nayi wanka nazo... "to sweet ♥ afito Lapia. Wani balcony yabi ya tura kofar ya shiga. d'akin babbane sosai kuma yasha sofa milk colour 's da carpet shima milk, kayayyaki dai Kamar d'akin mai mata, su dispenser, fridge, dasu frames iri iri... bandada tsinkewaba saida ya shiga bedroom, wani makadeden gadone yasha light blue d'in bed spread.. cire kayan jikinshi Yayi ya rage dagashi sai boxer, sannan ya bude bathroom yashiga... Kusan twenty minute Yayi sannan ya fito sanye da bathrobe da small towel Yana tsane kanshi.... wayarshi ya kalla a Saman bed side drawer sai sannan ya tuna da malama Nawaz... dauka yayi ya Fara dialling d'in number wayar daya bata, saida ya Kira Kusan so hudu sannan ta d'aga "Assalamu alaykum " me wayar baya nanne, tace cikin siririyar muryarta.... "malama ainine" cewar safraz. To safraz ya akayi? Kanne idonshi yayi sannan yace malama gani a bayi na cire kaya kuma ga ruwa a gabana, to ki fad'a min yadda zanyi... jin muryarta yayi tace "nashiga uku, wai wannan wane irin mutumne ❓❓ Sai kuma ta d'aga murya... kayi niyyah ka wanke hannu sannan ka yi tsarki saika wanke jikinta, d'in d'in yaji karar yanke waya... dariya yayitayi wallahi nakusa da alamu bazansha wahalar korar wannan ba.... farar armless yasa da wandon track suit da kadan ya wuce gwuiwa.... fita yayi zuwa falour, abinda malama nawaz tayine ya dawo mai Falour Ya shiga yana kyalkyale dariya harda rike ciki... sakin baki mummy tayi"sweetheart meke damunka. ai tambayar datayi saiyaji Kamar dad'a zugashi tayi.... sai dad'a kyalkyala dariyar yake... Assalamu alaykum, Muryar daddy Ta gauraye falour, da gudu safraz ya karasa ya rumgume dad oyoyo daddy kwana daya kawai kayi Amma Nayi mugun kewarka,,, mummy ta taso Ta amshi jakar hannun shi tayi mai Sannu da zuwa.. yauwa madam azo ayi feeding d'ina domin I really missed your delicious food... da sauri safraz yace "daddy yau nizan baka, dad yace to muje dining din saboda yunwa nakeji sosai.. warmer ya bude Yayi serving din fried rice ya zuba coleslaw a gefe. fara ba dad yayi Amma idan yabashi cokali daya Sai an kusa five minutes bai kara bashiba saboda tsabar surutu.. daddy ne ya gaji da haramiyar da safraz yake mishi "safraz tashi kaje dakina a drawer akwai wasu takardu ka dauko min.. Mikewa Yayi to daddy... Yana tafiya dad yaja plate d'in gabanshi ya cika spoon Sai baka.... dariya mummy taketayimai, Kallonta yayi "hajiya ainayi kokari ace bada abincine idan aka baka cokali d'aya sai anyi minti biyar, kidubafa kigani mintinmu ishirin Amma duka suka cokali Hudu yabani gashi inajin yunwa kuma abincin naki Yayi dadi... kuma cika spoon yayi yakai baki yanata kada Kai... tuni naga plate d'in babu komai... ruwa yasha sannan Yayi hamdala safraz ne ya fito rikeda wasu takardu....... kubiyoni donjin wacece umma.. kuma ya safraz zai kare da Malama Nawaz OUM AEYMAN CE 💖🎀🎀SAFRAZ 🎀🎀 Episode 3 Written by oum aeyman Safraz ne ya fito rikeda wasu takardu, Daddy ya naga ka tashi a dining d'in? "nakoshine shiyasa, Amma anjima saikazo ka kuma bani koh? Bata fuska safraz yayi, gaskiya dad baka koshiba, duka duka spoon nawa kaci? Dad yace "Allah nakoshi ,anjima zan kara ai....... 'bata fuska safraz yayi "shikenan dad ga takardun " Cewa Yayi to my handsome zauna anan mana.... Zama safraz yayi kusa da dad... "safraz kasan wadannan takardun meye ❓ "no dad ban saniba'' Dad yace "kakardun filin Dana siyan maka last year ne, shine da yake an gama ginin last week, Nakai aka yimin na gida.... Murmushi safraz yayi "to dad nagode and I am very very grateful, thanks once again.... dad yace " mention not my dear, ai ka wuce komai agurina.... Mum sai murmushi take tana jin dadi. E Eh eemm"gyaran murya dad yayi "fabulous yaushe zaka kawomin macen daka zabarwa 'ya'yanka? Safraz yace dad ban ganeba? Dad ya kuma cewa"i said when will you introduce the lady you choose for your kid's, to me ❓ 😢dad nifa nace Don Allah Adena wannan maganar domin ban Isa aureba.... Mum ce ta marairaice fuska "haba sweetheart, d'an Allah kayi hakuri mana, pls ka yarda kayi auren kai kanka zaka fi samun natsuwa da Lapia... Mikewa safraz yayi "nidai gaskiya bazanyi aure ba, fisbilillahi shekaruna 24 Taya zan iya ri'ke mace❓ dad yace haba fab kada Kace haka mana, nifa Lapia nake nemar maka, ko kafiso kayi tayin ciwo Kamar zaka mutu? hanyar dakinshi yayi ko bi takan zancen dad beyiba "nifa narigada nasan cewa a gidannan an dena kaunata, yaza ayi ace Nayi aure at this age of mine?? D'aki ya shiga yafada kan bed Yana Ta faman zancen zuci..... a falour kuma dad ne yake cewa mum "nifa abin yaron nan ya Fara bani tsoro, ace mutum baya tausayin kanshi,,, idan ciwon cikinshi ya tashi Kamar zai mutu Amma ana naiman mishi sauki shi baya nemarwa kanshi... mum tace "abinda za'a yi Alhaji shine kadaina yamishi maganar aure kwata kwata, domin na lura bayaso.. come on shut up " idan ya mutu fah? kinsan dai abinda likita yace koh? Mum tace "Allah ya baka hakuri Alhaji, wai dama ni bacin ranshine banaso...... Alhaji yace "my dear ai bakiyimin laifiba, fitinar Yaronne take damuna...... to Alhaji abinda za'a yi shine muyi ta addu'a insha Allah zamu dace, "domin addu'a'u sinanil mumin....... murmushi yayi "to madam muje ki had'a min ruwan wanka........ WAYEE SARFRAZ ❓ Alhaji muhammad (mahaifin safraz) kanuri ne d'an asalin garin maiduguri Yakasance shi kadai mahaifinshi ya haifa namiji saboda yayanshi bakwai amma duka matane shikadaine na miji.... Yana yiwa matan aure a shekara sha shida zuwa sha takwas Amma sai yace tunda Muhammad namijine zaiyi karatu mai tsawo, To Muhammad yanada kokari sosai, hakan yasa mahaifinshi yaje gurin chairman d'in yankinsu ya neman mai scholarship, Dayake yasan Manyan y'an siyasa ..... an kuwa dace ya samu Amma a Pakistan....... lokacin tafiya tazo suka tafi... yanata karatunshi cikin kwanciyar hankali har ya hadu da Wata bapakistaniya yar ajinsu.. sun shaku sosai da ita har soyayya Ta kullu tsakaninsu... sai Bayan dasuka kusa gama makarantane mumtaz (wato maman safraz take cemai ita batasan iyayentaba a gidan marayu ta taso, batada Kowa.... hakan data fad'a yasa ya Kara jin kaunarta ga wani tausayinta daya mamaye zuciyarshi achan aka daukeshi aiki a wani company Dayake Engineering ya karanta.... sanda ya dawo Hutu ya sanar da mahaifinshi labarin mumtaz shima ya tausaya mata sosai hakan yasa ya Kara karfafawa Muhammad gwuiwa..... Bayan Kamar Wata bakwai akayi bikinsu.... zama suke Lapia domin babu me bukatar tashin hankalin Dan uwanshi..... ana haka mumtaz ta samu ciki, murna gurin Muhammad babu magana shida danginshi domin duka suna kaunar mumtaz.... sunzo Nigeria sukayi Wata biyu, basu dade da komawaba nakuda ta kama mumtaz..... asibiti yakaita sannan ya Kira y'an uwa ya fad'a musu, mumtaz Tasha wahala domin kwana uku tana nakuda amma bata haihuba duk da likitocin Dake Kai kawo a kanta..... hakan ba karamin tararwa da muhammad hankali yayi ba..... kullum Yana cikin sallah da addu'a.... a ranar dasu mamanshi suka sauka mumtaz ta haifi danta namiji......... sai dai me😭😭 ita kuma Allah ya karbi ranta....... kuka gurin muhammad ba'a magana domin cewa yayi bazai kuma aureba, kuma duk sanda ya Kalli yaron (sarfraz) sai yayi ta kuka domin da mumtaz yayi kama, babu ta inda ya barta.... Cewa Yayi aikinma yadena.... Haka suka koma Nigeria..... Duk Muhammad ya lalace ko magana ma baya sonyi yarinyar wajen Kanwar babanshi wato kareemah itace tunda suka dawo daga Pakistan sarfraz yake gurinta, hakanan Allah ya Dora mata so da wata irin kaunar yaron, domin ko kuka Yayi yanzu hankalinta zai tashi watarana har tayashi takeyi.... ganin irin kaunar data keyiwa sarfraz yasa umman Muhammad takirashi ta bashi shawarar cewa ya aure ta domin tasan zata kula dashi da kuma d'an shi... Da farko Fir Muhammad yaki amincewada auren kareemah Amma daga baya Sai ya amince. anyi biki Lapia kuma suna zaune Lapia babu Wata Matsala, Hakurin kareemah yasa Ahankali sonta yarika shiga zuciyar Muhammad.... haka rayuwa tacigaba, sarfraz kullum cikin soda kauna ake nuna mishi..... domin Koda da wasa betaba sanin cewa ba kareemah (mummy) bace ta haifeshi saboda ita tsakani da Allah takesonshi ....... sarfraz ya taso irin mai ga'ba ga'ban jiki, ga Tsawo ga fad'i ga kuma wani irin kwarjini da Allah yayi mishi Yana zuwa citizen success academy Sannan kuma Yana zuwa HAYATUL ISLAM WA TATBIYATUL AULAD da yammah idan ya dawo daga boko... akwaishi da farinjini hakan yasa duk inda ya shiga sai ya zama star kafin yabar wajen. Yana dan shekara 17 ya tashi da wani irin azababben ciwon ciki ya Suma yafi sau goma... asibiti sukayi dashi mummy sai kuka takeyi... Saida aka kwana biyar ana fama sannan Allah ya kawo sauki, Bayan samun kan sarfraz din ne likita ya bukaci da subishi office d'in shi yanaso suyi magana.... anan ya shaida musu cewa sarfraz ya samu cells problems Wanda ya haifar mishi strong sexual desire ... kuma abu d'ayane zai warkar mishi da shi shine kawai amishi aure, idan ba hakaba ciwon zai iya Bata mishi wasu gabobin jikinshi koma yayi silar mutuwar shi.... Bayan an sallamesu sun koma gida daddy da mummy suka yi mishi bayanin abinda Ke damun shi sannan sukace zasu yi mishi aure.... kuka sarfraz ya ri'kayi har abinci ya denaci.... hakan yasa sukabar maganar gaba d'aya... Kuma duk sanda suka taso da maganar sai rai ya baci...... malam Auwal shine malaminsu a HAYATUL ISLAM... saura shekara daya suyi sauka Allah yayi mishi rasuwa.. aka kawo musu wata malama, cewa sukayi bata yimusu ba.... haka malam Abdullahi (shugaban makarantar) yayita chanza musu malamai Amma saisuce basu musuba.... har saida ya gaji ya daina chanzawa.. sukuma suka fara korarsu da rashin kunya da kuma tambayoyi.... fir sunki yarda amusu graduation, kuma sun haddace QUR'AN sama da shekara uku,, duk sanda malam Abdullahi ya musu magana sai suce su murajia sukeyi..... ana wannan chakwakiyar ne aka kawo musu malama nawaz.... Cigaban labarin........ Tana yanke wayar ta hau Tsaki waishi wannan wane irin fitsararre ne? Ace mutum babu kunya babu Ta ido.... sallar isha'i tayi sannan ta koma ta kwanta washegari 4:04pm Malama nawaz ta shiga IBN KHATHEER. sallama tayi "sannunku y'an aji. "yauwa Sannu malama.... QUR'AN taciro ta Fara karatu.... sarfraz yace malama Don Allah kiyi hakuri "jiya munyi miki karya domin dukanmu surar mu d'aya...... mamakine ya kama nawaz "wai kana nufin jiya wahala kuka bani ❓ cewa sukayi "malama Don Allah kiyi hakuri wallahi bazamu kumaba.... aranta tace tab Anya kuwa sunada hankalima kuwa? tambayarsu surar da suke tayi sannan ta karanta musu...... fiqhu ta dauko zata karanta.. safraz yace malama Inada tambaya.... banza tayi dashi domin tasan kwancen haukar shine ya motsa.... da karfi yace malama don Allah.... cewa "tayi sarfraz inajinka meye? malama dama jiyane na fadawa dad dina cewa kince amin aure, shine yace to zaiyimin Kwanan nan... to yanzu inaso ki Koyamin yadda ake kwanciya da Mace da kuma Adduar da akeyi kafin a kwanta da ita... sannan kuma Don Allah kisiffantamin harijar Mace saboda kada inje in aureta bansaniba, domin na tabbata kasheni zatayi....... shiru tayi saboda wata irin kunya da fargaba da suka kamata lokaci daya dago da kanta tayi "safraz wannan ba irin tambayar da ake yi bace.. ya kamata kaje kasuwane ka siyo kitabul jimah duk zaka gani a ciki... "malama ai bansan inda zan samuba... "cewa tayi inadashi zan kawo maka gobe..... to malama Inada wata tambayar Amma ba irin waccan bace... "inaji" nawaz tace malama dama cewa nayi idan na kwanta da Mace da gaske Sai kuma banyi realising ba kenan bazanyi wanka bako? Tsawa ta daka mishi "ya Isa safraz!!! kallon juna sukayi shida Abdul suna kannema juna ido 😉 fadila ce ta Mike "malama Don Allah yasunan kakar fir'auna da kuma sunan innoninshi da sunan kawunnanshi da sunan abokanshi da sunan unguwar zamanshi? cewa tayi "bansaniba domin ranta ya baci da tambayar da safraz yayi mata. usman ya kuma Mikewa "malama Don Allah shekara nawa da halittar duniya sannan kuma saura shekara nawa Ta tashi? shima cemai tayi "bansaniba " Abdul ya mike "malama Don Allah shekarar ki nawa? banza tayi dashi, dada cewa Yayi kuma don Allah ya akayi kika samu koyarwa a makarantar nan...... Bata kulashiba , ganin haka safraz ya kuma Mikewa "malama ance mata masu tsawo da kuma dogayen yatsu da diri me kyau sunfi dad'in sha ani lokacin saduwa? Jakarta ta dauka ta fita bata ko Kalli mutum d'aya ba.... tana fita suka dau tafi yeeyyy munyi nasara.. safraz dai Sai murmushi yakeyi... gaban Ajin yazo pls Kowa Yayi shiru ya saurareni....... kubiyoni donjin shin nawaz zata dawo kuma shin me safraz ze cewa y'an Ajin OUM AEYMAN CE 😉*🎀🎀 SAFRAZ 🎀🎀* *Episode 4* Written by oummou muhsien✍️ Supreme writters association........... Gaban Ajin safraz ya karasa "Kowa Yayi shiru ya saurareni....... Hmm a gaskiya yau ina cikin farin ciki, domin kunyi ko'kari sosai, saboda abaya ni kadai kuke bari nayita fama shiyasa ba'a samun damar korar su da wuri Amma yau Kowa ya tofa albarkacin bakinsa naji dadi matuka kuma Kun nuna min cewa ana tare, dama hausawa sunce sarkin yawa yafi sarkin karfi...... Nasan cewa wannan fitar datayi ta fita kenan baxata dawoba kuma koda director da kanshi ya bata hakuri bazata yarda ta dawoba saboda abin yasha karfin kwakwalwarta....... Yanzu mu saurari abinda zai faru gobe.... Bayan Nan kuma saimu shirya walimar da za'a yi ta cin nasarar mu Cheers 👏🏼👏🏼👏🏼👏👏👏 sannan Yayi hanyar Waje sauran y'an Ajin suka rufa mishi baya....... Motarshi ya shiga zuwa gida Amma abin mamaki shine ko Sahun malama nawaz be ganiba, Sai kuma yaji beji dad'in hakanba..... Koda ya Isa gida sai yajishi duk acikin damuwa komai ma a sanyaye yakeyinsa "Anya kuwa na kyauta abinda nayi, Anya ban zalunci kaina da itaba? Ai kodon darajar Qur'an din da take karantawa yaci na rabu da ita, to koma dai damuwace ta sata koyarwar? Tun abin be nunaba har Saida mummy ta gane "sweet heart meke damunka? "Mummy babu komai, kawai dai banjin dadine" "Fab don Allah in wani abunema ke damunka please kada ka boye min, idan baka fada min ba wa zaka fadawa? Duk duniya bamuda Wanda yafi junanmu, idan Kanada damu ka fada min saimu naimi mafita. Kuma dama inaso na Maka magana gameda auren da dad Dinka yakeso kayi "gaskiya hakurin shi ya soma karewa, kuma naga auren ma is for your own good, please ka duba maganar "To mummy insha Allah kada ki damu zan duba" ya Fadi Hakan ne kawai don ya Yankee maganar bayaso tayi tsawo NAWAZ........... A kufule ta shiga gida ko umma Dake zaune a tsakar gida Bata kalla ba balle tayi mata Sannu da gida. A falour Ta tarar da ummi tana ninke kaya "Sannu da aiki ummi" abinda ta iya cewa kenan Ta wuce dakinta... Jefar da jakar tayi a Kan gado ta tuge niqab da hijab d'in a tare..... Kan gadon ta fada "wai wadannan wasu irin yarane Allah ya had'a ni dasu? Ace mutum beda kunya beda Ta ido, Kowa duk maganar datazo bakinshi haka zaike fad'a min ita! Amma zanyi maganinsu, wani tunani ya Fado mata "Anya bada gayya sukemin wannan iskancinba? Idan kuwa hakane zasu gane shayi ruwane, don bazan bar makarantar ba saina koya musu hankali. Mikewa tayi ta fita falour, a kofa ta hadu Da ummi zata shigo "nawaz wai Meyafaru naga kin shigo ranki a bace??? Ummi wallahi y'an ajinane, na gaji da rashin kunyarsu na gaji da wulakancinsu basa da kunya ko kadan........ nawaz koda yaushe Ina yawan umartarki da yin hakuri duk fa Wanda kikaga yayi nasara a rayuwa sai yayi hakuri tukuna, Dan Allah kiyi hakuri kici gaba da zuwa aikin Nan da kika samu rufin asirine a gurin mu... wallahi mutane basason aikinnan dakika samu kuma idan har kika bari to kinga burinsu ya cika kenan son haka nake umartarki da ki jure kuma ki toshe kunnuwan ki akan duk wani abu da zasuyi ko auce, illa ke dai kiyi abinda ya kaiki ki dawo gida..... To ummi zanyi duk yanda kikace indai zakiyi farin ciki, amma inaso ki kara yawan Adduar dakikemin akullum domin ita zata karamin samun nasara a rayuwa..... to nawaz Insha Allah zan 'kara akan wadda nakeyi, yanzu Maza ki tashi kije kiyiwa umma Barka da gida domin inajinki sanda kika dawo baki gaishetaba... to ummi " Mikewa tayi ta fita. A kofar d'akin umma taita sallama Amma ba'a amsaba, Saita yanke shawarar ta shiga cikin d'akin...... Tashiga ta nufi hanyar bedroom d'in umma, Amma ga mamakinta abinda taji shine : "Tunda Rahma Ta yarda Ta auri mijina wallahi ita da kwanciyar hankali har abada, kuma yarinyar data haifa ita Zansa ta zame mata bala'i da annoba a rayuwar ta saitayi burin mutuwa akan rayuwa, na tsani Rahma na tsaneta wallahi don kawai bazan iya kasheta bane Amma da tuni na kashe shegiya. Amma dukda haka saina dasa mata tabo a rayuwarta Domin nawaz bazata ta'ba yin aureba har abada kuma badai Alhaji ya tafiba to kuwa shida ya dawo Sai ruwan daza su Kai bakinsu ya gagaresu.... Muryar fauziyya taji tace umma kidena damun kanki da wani zancenau domin bokan yacemin duk abinda kike Bukata zaiyi miki hardai akwai kudi...... umma tace " fauziyya wai jiya saiga yaro ya shigo gidannan wai ana sallama da nawaz....... Idan kinji yanda zuciyata ta kusa fashewa saikin tausayamin tsabar bakin ciki da damuwa Saida na Dena ganin gabana, kuma Baki saniba wai Dana leka mutumin harda mota alamun Mai kudine sosai duk da a duhu ne Amma bakiga yadda shaddarshi ke kyalliba..... Daria fauziyya tayi " nace ki kwantar da hankalinki kuma ki kaddara cewa wannan kiran da aka yi mata jiya shine kiranta na karshe son wallahi yadda ban auri me kudi ba Bata Isa ta aura ba, ai wahalace ta dace da ita ba niba.... "umma tace nifa Dan bokannnan yace bazatabi duniya bane Amma wallahi ni a yanda natsaneta naso ace ta zama karuwane tana haifar shegu uwarta na mata raino da goyasu, yanda ba'kin cikintane zai kashe uwarta har lahira........ Amma dukda haka babu komai "tashi mu koma falour zan duba inga abinda ya dace muyi ni matsalata kudin da bokan ya bukata sunyi yawa "Hmm umma biyan bukata yafi dogon buri kawai ki bashi ayi komai a gama" cewar fauziyya tana duban umman...... da sauri nawaz ta fita tana mamakin maganganun umma "dukda bayau ta Fara jinsuba amma nayau sun d'aga mata hankali matuka,. To wai ita meye laifinta? Ba ita ta zabarwa kanta uba ba ..... ruwa ta d'iba a buta donyin alwala , Tana cikin wanke fuska wani yaro ya shigo "wai wani mutumi a waje yace aunty nawaz tazo! ha'ki'ka nawaz taji dad'in kiranta da akayi kodon ta kuntatawa umma zata fita kuma koma waye zata tsaya Ta saurareshi tunda Taga abin na umma dada yin gaba yakeyi. Da sauri tacewa yaron "je Kace tana sallah Amma yanzu zata fito ... to yaron yace sannan ya fita a gur guje ta karasa alwalar ta shiga d'aki donyin sallar, sai sannan umma da fauziyya da suke labe Bayan labule suka fita Don ganin waye yazo gun nawaz din... "ga mamakinsu kyakykyawan matashi Mai karfi a jika suka gani jingine da mota da waya a hannunshi Yana dannawa kumA da alamu kudi sun zauna Mai sosai duba da irin sututar Dake jikinshi, da irin Motarshi da kuma yanayin shigarshi... Kwafa umma tayi "fauziyya Bana jiya banefa gaskiya ya kamata ayi wani abu domin wallahi ciwo zai iya kamani muddin aka cigaba da Haka kada fa yarinyar Nan ta auri Mai kudi.... cikin gidan suka koma suna tafe suna kulla makirci (Allah kasa Mufi karfin zuciyarmu, wai uwa da yane suke wannan Al'amari) Bana Jin Dadin jikina kuyi manage da wannan _*YAR CHIKAJI*_✍️✍️*🎀🎀 SAFRAZ 🎀🎀* *Episode 5* Written by oum aeyman Supreme writers association...... We write with the ink of era...... Cikin gidan suka koma suna tafe suna kulla makirci....... Nawaz ta fito sanye da niqab, ta fita Waje A Gefe ta hangoshi jingine da mota.. Karasawa kusa dashi tayi "Assalamu alaykum" "wa'alaykis salaam" yace yana murmushi..... "meya kuma kawo ka gidanmu? What did you come for? Dariya safraz yayi "am sorry aunty nawaz I'm really sorry please, "it's okay, now tell me what are you up to? Truly I'm not up to anything malama Dariya nawaz tayi "really? Wallahi Dagaske nake ba komi, dama daddy nane ya aikeni shine nace bari na biyo mu gaisa.... OK nagode sosai safraz, kasamu ladan ziyara, I will be getting inside now... No malama pls don't go,... Dariya abin yaba nawaz yanayin yanda Yayi magana Kamar karamin yaro, dakewa tayi "why"? "Saboda akwai maganar danakeso muyi".... "Okay inajinka Menene? "Ehm dama cewa nayi ni kadai mummy na ta haifa banada kanwa ko yaya.... To what's wrong with that? Nima ni kadai ummina ta haifa.... "Yauwa kinga faduwa tazo dai dai da zama kenan koh, yanzu Sai mu zama y'an uwan juna koh? Bata fuska nawaz tayi "as how? Dariya safraz yayi saboda ya gane me take nufi "as in inzama yayan ki Ke kuma kanwata, kinga that will be I have a sister and you have a brother, right? Murmushi nawaz tayi "Sannu Dason girma har kawani zabarwa kanka yaya to gaskiya bazan yardaba I will be the senior sister .... OK Kowa ya fad'i shekarunshi, kinga duk Wanda shekarunshi sukafi yawa shi zai zama yaya... "it's okay I'm 25yrs how about you? "Lallai malama dama Haka kikeda son girma ? Ina laifin ma kice 20yrs " bawannan ba Kai nawanaka? I'm 24yrs old,,, hmm Sannu "wai kai gudun shekarun kake? "No malama I'm serious.... "Okay nima I'm serious me zan samu idan nayi Maka karya? "A'a malama duk maganar batakai namba, naji zan zama 'kani saiki zama yaya. " Don't worry nabar maka girman, Allah yasa ka iyayin abinda yaya yakewa kanwa ..... "amen sister, Allah yasa, kuma nagode da kika amsheni a matsayin yaya.... to zan shiga gida kaga an Fara kiran isha'i, zanje nayi sallah.. malama please Dan tsaya,... bata rai tayi "naga na saurareka, an then what next? ba komai malama dama cewa nayi ki tsaya ki amshi present Daga yayanki.. wani karamin parcel ya ciro d'aga cikin mota ya mika mata gashi sisyna, and please meyasa har da dare bakya cire niqab, aiya kamata ki cire kodon kiji iska no, i can't take anything from you! And kuma niqab raayi nane why sis? Pls consider this from your brother not from your student....and zancen niqab kuma kiyi hakuri banyi Don na bata miki raiba Amsa tayi tace thank you, good night... harta juya ta waigo "yauwa safraz tsaya in dauko maka wayanka, No malama kibarshi i will take it when i am ready .... "to"tace sannan ta yi hanyar gida.... Dasauri umma da fauziyya suka shiga gida har suna gware saboda kada nawaz ta gansu,, safraz be tafiba har saida ta shiga gida sannan ya shiga mota, A masallacin dake kusa dasu yayi sallah sannan ya shiga gida... A falour Ya tarar da mummy tana safa da marwa.... tana ganinshi ta rungumeshi hade da ajiyar zuciya "haba sweetheart Daga cewa bari kazo yanzu zaka dawo shine har kafi one hour? Wallahi duk hankalina ya tashi, Dariya safraz yayi "kada ki damu mum gashi na dawo, ina dad? 🤫🤫tun dazu ya dawo, yace Ina Kake shine nace mai kana daki kana kararu saboda nasan zaiyi fad'a idan yasan nabarka ka kuma fita Bayan ka dawo daga islamiyya... yanzu abinda za'a yi ka shiga d'aki kayi wanka anjima saikafito amatsayin ka gama kararun.. rungumeta Yayi ya sumbaceta a goshi "I too much love you my love.... sannan ya wuce Yana Daria..... Cewa tayi kayi sauri ka gama abinda zakayi da wuri saboda kasan gobe Monday kuma kacemin kanada test koh d'aga mata Hannu Yayi "as you command my only queen kwallace ta fito mata a ido, tayi sauri ta goge, zancen zuci ta Fara "bansan yanda sarfraz zaijiba duk Randa yasan cewa banice asalin mahaifiyarshi ba.... hanyar d'akin daddy tayi tana dada goge idonta.... NAWAZ....... koda tashiga gida d'aki ta wuce, a falour Ta tarar da ummi tana sallah dakinta ta shiga ta ajiye parcel d'in a Saman gado... Sannan ta shimfida praying mat Ta fara sallah, Bayan ta idar ta fita wurin ummi sunata hira, acikin hirarne ummi tacewa nawaz wai waye yazo gurin kine dazu? "ummi wani senator ne, abin har tsoro ya bani domin ba anan yake zamaba yana zamane a Liverpool can kasar ENGLAND... Amma gaskiya bazan amince mishiba domin bazan tafi nabarkiba coz you're my everything my love, my hope, my role model, my World, my desire...... Daria ummi tayi "to shikenan kiyi Ta addu'a Insha Allah nima zan kara a wadda nakemiki kuma idan Allah yayi mijinkine hakanan Zaki tafi ki barni... Rungumeta tayi to my sweet mum I love you so very much.... (me karatu zaiso yaji meyasa nawaz ta shirgawa ummi karyako? umma tayiwa karya ba umminta ba, domin tun sanda nawaz ta fito daga d'aki Ta hango umma da fauziyya labe a Gefen window, shiyasa tace haka kodon Ta sosawa umma zuciya. sai gurin goma suka gama hira, ummi ta shiga dakinta sannan Nawaz ta shiga nata itama... asaman gado taga parcel d'in sai sannan ta tuna da zuwan sarfraz "wai meyasama na saurari sarfraz ne? (wata zuciyar tace saboda kibatawa umma rai mana) To Amma yanayin maganar da mukayi ta dace? Kawar da tunanin tayi ta bude parcel d'in Don ganin Menene aciki Me karatu ka biyoni donjin me safraz ya bawa malamarshi Ciwon Kai🤯*🎀🎀 SAFRAZ 🎀🎀* *Episode 6* *Written by oummou muhsien* ✍️ Supreme writers association....... We write with the ink of era....... That's era is our ink 😉 Bude parcel d'in tayi Don ganin Menene aciki... Ga mamakinta takardu tagani da yawa sannan kuma sai Wata karamar jaka a ciki mai kyalli.. Bude jakar tayi, zoben diamond 💍 ne mai kyau aciki. A yatsanta na kusa da karami ta gwada cikin Sa'a kuwa yayi mata dai dai. Yatsan taketa kallo don zoben ya matukar burgeta suka cewa batasan kudin shi ba. Takardar farko ta dauka ta fara karantawa kamar haka..... Assalamu alaikum Malama Don Allah Kiyi hakuri da abin da muka yi miki. Insha Allah bazaki kuma samunmu da makamancin abinda mukayiba...... Zainab kabir Ta biyu ta dauka itama exactly abinda aka rubuta ana farkon amma saidai sunan ba d'aya bane.... Haka tayita bin takardun har saida takai ta karshe...... Assalamu alaykum... Malama Ina mai neman afuwarki kuma Ina cike da baƙin ciki da Dana sannin abinda mukayi miki musamman ma ni... Don Allah malama kiyi mini aikin gafara, Kuma Don Allah kada ki dena koyarwa a makarantarmu domin idan kika dena zuwa nima nadena zuwa islamiyya har abada..... Ina Fatan zaki yafemin....... Nagode Sarfraz Muhammad goni...... Murmushi tayi "Mtswess yafi Kowa neman magana da rashin kunya Amma yafi Kowa zaƙin baki da neman yafiya, saboda in koma sucigaba da garani Kamar kwallo... Zoben yatsanta ta kalla sannan tace to zobenma meye manufarshi kuma Oho? nidai na gaskiya zoben 💍 yamini kuma bazan cireba.... Takardun Ta tattara Ta mayar dasu cikin parcel d'in ta ajiye a saman drawer.... addu'o'i tayi sannan taja bargo ta rufa...... Nawaz saimuce safiya ta gari 🌠🏝 MORNING........ 8:30AM 🔅🔅🔅🔅🔅🔅 SARFRAZ........ zaune yake a dining Yana cin French toast da stir fry noodles, saboda idan zashi school yafison yaɗanci abu me nauyi coz he's not use to abincin Waje..... mum ce tafito rike da black back pack,. Turus Ta tsaya "sarfraz wai meke damun Kane? Kacemin 9:00am kakeda lecture kuma test Kace za'a muku amma yanzu har to 9 Amma kaƙi tashi ka tafi.... Shiyasa nafiso ka tafi da dad dinka wallahi. mum kiyi hakuri wallahi abincine da zafi kuma bake bace kikaki bani kikace naci da kaina...... Hmmm bansan Randa zaka girmaba sarfraz, ruwa ta tsiyaya a tumbler ta mika mishi yi sauri kasha ruwan nan.. Amsa yayi yasha sannan ya amshi back pack ɗin yasa a baya yayi hanyar Waje yana murmushi "bye my love " Ɗaga mishi hannu itama tayi tana murmushi "bye 👋 sweetheart.... motanshi kirar Honda continue discussion fara yahau.... Reverse yayi gate ya bude Yayi hanyar University dinsu..... NAWAZ............ EXACTLY that morning, share dakinta tayi sannan ta fito ta share d'akin umminta da falour ta gyarasu duka... Turaren wuta ta kunna sannan ta fita ta share tsakar gida ta wanke duka bayin gidan.... Ɗaki Ta koma ta shiga kitchen..... sanwan taliya da wake tayi sannan ta dawo falour Ta zauna tana duba hisnul Muslim dinta. sallamar Khadija taji (wadda sukayi B.ed a F. C. E tare) da sauri ta tashi suka rumgume juna.. Khadija tace "nawaz kwana biyu kin gujeni ko wani abu nayi miki? Murmushi nawaz tayi "habadai niko me zakimin kawaidai ban cikason zuwa gidan matan aure bane kuma kinga nasamu koyarwa a HAYATUL ISLAM..... "ikon Allah saikace Kema watarana bazakiyi auren ba, kinga muma saimuki zuwa naki gidan. Cewar Khadija tana hararar nawaz... Dariya nawaz tayi sannan ta tashi ta kawo mata ruwa da d'an abin motsa baki.. sannan suka zauna aka fara hira...... niko nawaz ina ummi? tana barci Amma nasan takusa tashi tunda goma tayi .... Abincin ta sauke ta zuba musu suka faraci suna hira jefi jefi... ummi ce ta fito daga dakinta tana Gyara dankwalin kanta.... "A'a Khadija yau kece a gidannan? kwana biyu ban ji duriyarkiba.... murmushi Khadija tayi "wallahi ummi kwana biyu banga kawar Tawaba shine nazo Biko..... dariya ummi tayi tace "aikuwa kin kyauta ya megidan baki fatan duk kuna lafiya? " Lafiya lau ummi"... "Masha Allah haka akeso" cewar ummi sannan ta wuce kitchen..... sai wurin Karfe biyu Khadija ta tafi gida.... Nawaz ta dawo daga rakata suka hadu Da umma a zaure, dagewa umma tayi ta rusa ihu "wayyooooo zata kasheni...... Nawaz ko abin mamaki ya bata ta tsaya tana Kallonta. Ummi ce ta fito zauren da gudu tana tambayar Lapia? Ga tsinanniyar datakeson ganin bayana nan ace kamarni zan wuce bazata iya kaucewa ba saidai mu bangaji juna saboda tsabar rashin tarbiyya..... hakuri ummi ta bata da nufin Insha Allah baza'a kuma ba domin zatayima Nawaz magana.... hannun nawaz ta rike suka shiga d'aki, "wallahi ummi ban bangajetaba. ummi tace yi shiru nasan halinki, bazaki taɓa bangaje waniba balle umma. nidai abinda nakeso dake shine Don Allah ki kara kula sosai, ki rika kiyaye wa. Kuma dama inaso na fada miki cewa jibi zan tafi maiduguri....... "da sauri Nawaz tace ummi saboda mene? Amma dai Dani zaki koh? A'a Nawaz badake zaniba saboda kinga kinada koyarwa dakikeyi kuma idan baki koyarba kinsan bamuda abincin da zamuci, kinfi Kowa sanin halin da muke ciki kuma kinsan dai ko wata daya da tafiyar mahaifinku ba'ayiba ta rufe store wai abinci ya kare.. Yanzu ko kinsan watanshi sha d'aya da tafiya, babu zuwa babu aike kuma ko wayarshi muka Kira bata zuwa shine nakeso naje, idan naje gidanmu sai inje gidansu inji ko lapiya amma zan cewa umma Kano zani inna batada Lapia saboda idan na fada mata cewa maiduguri zani Saita San yanda zatayi Ta hanani zuwa... "to ummi Allah yakaiki Lapia ya dawo dake Lapia, jibi kikace zaki tafi koh? Ummi tace Eh nawaz d'an Allah kiyi hakuri da halin ummanki kinji sati daya kawai zanyi Insha Allah.. Murmushi Nawaz tayi "to ummi Insha Allah babu abinda zai faru, zan kiyaye 3:00pm A gajiye sarfraz ya shiga falour Yana tafe yana tangadi Kamar Dan Maye, Mummy ce ta rikeshi da sauri "meyafarune sweetie? bata rai Yayi "mum I'm exhausted, kuma kinsan cewa lecturer nan banzoba Sai wurin Karfe d'aya, saboda yanaso mu tafi ya bamu carry over..... cewa tayi Sai ka dada hakuri kaga kana last year ne saida kauda kai koh my boy? Murmushi yayi "mum me kika dafa mana ne yau? White rice and chicken stew hope zakaci? Eh mummy zanci Sosaima saboda yunwa nakeji sosai... Dining ta jashi sannan ta yi serving dinshi "yi sauri ka ci saikayi wanka kaga lokacin islamiyya yayi. To yace sannan ya Kara yawan abincin yanaci da sauri... Saura kadan ya cinye ya mike "mum nakoshi bari Nayi wanka. OK to kayi sauri kaga saura ƴan mintuna Hudu tayi kada kayi latti.. HAYATUL ISLAM...... Malama Nawaz nagani zaune a teacher's seat, rike da Quran tana budewa dai dai nan safraz ya shigo rike da hulanshi a hannu, gabanta ya karasa sannan ya ɗan rage tsawon shi malama don Allah ayimin afuwan rashin zuwa na dawuri daga school nake. Ɗaga mishi hannu tayi "babu komai jeka seat dinka... tashi Yayi yaje seat dinshi ya zauna..... abin yaba nawaz mamaki domin gaba ɗaya yau tunda Ta Fara karatu har tagama babu Wanda ya tambayeta, kuma babu alamun rashin kunya a tare dasu... Adduar tashi tayi ta fita, da sauri sarfraz yabi bayanta, "malama Dan Allah in kaiki gida mana... waigowa tayi "A'a sarfraz nagode kabarshi, nema Yayi ya matsa mata, ta wuce ta bashi guri.... Haka Koda ya dauko mota yayi ta binta ita kuwa tayi banza dashi. har takai gida yana binta..... Yau Ta kama ranar da ummi zata tafi maiduguri, fitowa tayi ta fada wa umma cewa zataje kano gurin innanta batada Lapia kuma Kila tayi sati daya... murmishi umma tayi saboda ita kadai tasan abinda take ƙullawa a zuciyarta "Allah ya kiyaye hanya kuma Dan Allah ki gaishemin da ita, kice ina mata Sannu.... Har Tasha Nawaz ta raka ummi, inda ummi keta jaddada mata kada ta sake tayi abinda umma zata ce ta mata rashin kunya, dakyar Nawaz tabar Tashar Ta koma gida........ tunda Ta shiga gida bata fitoba saida zata islamiyya... tana fita umma tadauki waya "hello Eh ina Tasiu,? To Kai mishi wayar Kace mishi maman su Fa'iziyya ce tanaso zasuyi magana ne..... Wata muryace irin da ƴan sigari tace "hello hajiya " " Tasiu yagida? Lapia lau hajiya, ya aiki? Lapia lau Tasiu, wani aiki nakeso kayimin Dan Allah ... to hajiya inaji Ina nawaz yarinyar kishiyata? Eh hajiya Na ganeta, meya faru? ba kwanaki kacemin kana sontaba... Eh hajiya anyi haka. to dama ce ta samu, kaga idan baka auretaba saika cire kishirwa ko kuwa? "Hajiya banganeba? "Ehm Ina nufin mamantace tayi tafiya yau, shine nace kozakazo da dare zan barmaka kofa a bude kaga saika shiga ɗakin kayi Sha'anin ka, kuma kaga ita kadaice babu mai taimakonta...... hahahahahahahahaha hajia kenan gaskiya nagode da wannan damar da kika bani zan kuwa Kore ƙishi sosai, faɗa mishi yanda za'a yi tayi sannan sukayi Sallama ta yanke wayar (Ya Allah kasa mu dace ace wai ƴar mijinka zakasa ayiwa fyade saboda baƙin kishi) NAWAZ.... Koda taje makaranta haka take sukuku , ko Daliban ta saida suka lura tana cikin damuwa,, Sarfraz ne yace "malama don Allah meke damunki, dukda bama ganin fuskarki Amman yanayin move ɗinki ya nuna kina cikin damuwa... cewa tayi "safraz babu komai mamanace tayi tafiya shine nakejin kewarta .. Kowa addu'a Yayi mata cewa Allah takaita ya kuma dawo da ita Lapia, nan danan nawaz ta saki suka cigaba da karatu cikin raha.... zainab tace " malama Dan Allah yaushe zaki nuna mana fuskarki? dariya tayi tace gobe (tace hakanne Don abar maganar) nan duka y'an Ajin suka dau kuwwa Kowa yana murna zaiga fuskar malama nawaz... cewa tayi ya Isa ya Isa yanzu mucigaba da karatu..... yauma Kamar jiya koda aka tashi sarfraz ne biye da nawaz yana rokonta akan ya kaita gida, ƴan aji Kowa mamakin chanzawar sarfraz suke domin ya dena yi mata rashin kunya kuma yaƙi basu dama su tambayeshi dalili saboda da antashi shima zai tafi gida ba kamar da dayake tsayawa yi musu lecture ba. still har gida ya bita, saida ta shiga gida shima ya tafi... Bayan tashiga gida tayi sallah tayi karatu sannan tayi sallar isha taci gaba da Duba littattafan ta. wurin Karfe goma taji cikinta ya murɗa... cewa tayi A'a niko me naci cikina zai lalace da tsakar Daren nan, gashi banason fita wallahi.... hakanan ta bude Kopa ta fita, tanashiga bayi su Tasiu suka shigo gidan. Bayan Kamar minti biyar ta fito, ajiye butar tayi a bakin fampoo sannan ta shiga d'aki tana d'aga labule Ta hango mutum da torch 🔦 Yana haska dakunan faloun.. cewa tayi waye? nufota yayi gadan gadan, baya ta farayi Yana dad'a biyota. wani ta gani shima ya fito daga dakinta cewa yayi "shegiya itace riƙeta... da gudu tayi Waje, suma suka rufa mata baya, tsakiyar titi tabi da gudu iya karfinta tana mamakin me waɗannan yan daban zasu yi mata a tsakar daren nan. SAFRAZ..... AROUND 10:00PM bude dakinshi Yayi ya fito falour, kitchen ya shiga ya bud'e freezer, murfin freezer ya buga "damn it yanzu ace duka gidannan babu lamun tsami ko guda daya? mtsews yanzu yazanyi? Falour yaje ya zauna yayi shiru ya hada Kai da kafa... mum ce ta fito daga d'akin daddy rike da mug da alamu coffee zata had'a mishi .. sarfraz ta gani zaune Saman couch yayi uban Tagumi.... sweetheart meya faru naganka zaune anan bakayi barciba? "mumy wallahi kitchen naje kuma babu apple 🍎 babu pear 🍐 babu berries babu wani abu dazan iya ci, kuma na kasa barci.... sweetheart matsalata dakai kenan, Haka kake Kamar mai ciki idan Kace kanason abu to baka ta'ba samun kwanciyar hankali saika samu abin.. yanzu yakakeso ayi? mum kawai kibari inje fresh vitamins nasan zan samu yanzu tunda kinga su Sai twelve suke tashi... kanka d'aya sweet heart? yaza ayi inbarka kafita yanzu Bayan goma ta wuce? "mum yanzufa zanje na dawo wallahi idan banci apple dinnan ba bazan iya barciba, please mum ki tausayamin.... okay naji amma dai gaskiya kayi sauri kuma kada ka bari daddy yasani saboda zaiyi fad'a.... Dasauri ya mike Yana murmushi "thank you so very much my dear, I love u fita yayi zuwa parking lot Yana hamdala da Allah yasa mummy ta barshi domin yasan idan bai samu lemun tsamin yasha ba babu shi babu barci ayanda yake jin feelings na tasomai, yadai cewa mummy apple ne saboda yanajin kunya. Tada motar yayi sannan ya fita ya dauki hanya, yazo shan corner ya hango Kamar mutane sun wuce da gudu,, mamakine ya Kamashi "su waye Ke gudu da wannan tsohon Daren..... ya juya zai cigaba da tuki yaji muryar Mace tana ihu "wayyo Allah na Mena muku, Dan Allah ku kyaleni..... juya motar yayi yabi Bayan su, Maza biyu yagani sun rike wata yarinya, ɗaya ya rike hannun ta na hadu, ɗaya kuma ya bankare hannun dama ..... parking yayi nesa dasu, sannan ya fito Yana tunanin mezai dauka Wanda zai taimakamai wajen kwace yarinyar... Hammer 🔨 ya hango a cikin mota, da sauri ya dauka yabi bayansu, kafin ya karasa yarinyar ta kwace kanta ta ruga da gudu.... yanayin firgicin datake ciki yasa bata lura da poll wire d'in dake gaban taba.. jikake kummm taci Karo da ita, aikuwa take ta zube kasa a sume kasancewar poll wire ta karfe ce.... dariya suka kyalkyale da ita "duk gudunki gashi Mun kamaki a sadaka.... kinga azaba ta farfad'o dake koh???? dai dai nan safraz ya karasa kusa dashi, d'aga kasan hammer din Yayi daidai handle ya zabga mishi a tsakiyar kai... faduwa Yayi yana shure shure kasan cewar Wata sabuwar azaba dayaji Ta ziyarci kwakwalwarshi.... Dasauri Dayan ya ciro wuka a kugunshi ya nufi safraz da ita.... d'aga hammer ɗin safraz ya kuma yi ya buga mishi a hannu take Wukar ta fad'i, shi kuma ya dafe hannun yana ihu, dad'a buga mishi yayi a gwuiwa shima ya fad'i. Daidai nan na farkon ya mike ya ruga da gudu, ganin idan ya bishi dayanma na iya guduwa yasa ya tsaya.. kafarshi ya d'ora mishi a kirji ya taka da karfi, ku wasu irin Marasa imanine, ace Mace kukebi zaku ciwa mutunci, irin Kune Marasa kishin Addini ko... a wuyanshi ya d'ora kafar "me yarinyarnan tamuku kuke binta haka? kakari ya Fara 'Aa a a a zan fa...d... 'aaa, d'aga mishi wuyan yayi yace faɗa inajinka, kishiyar maman Yarinyarce ta Kira ogana tace muzo muyi mata fyaɗe.... shine mukaje gidan tagudo Waje mu kuma muka biyota... "Hmmm Allah ya shirya ku". Kyaleshi Yayi ya karasa kusada yarinyar.. Kallonta yayi helplessly dakyar take iya numfashi... amma gata very beautiful and charming, tashi ɗaya yaji ta burgeshi.... da sauri ya suƙa ya dauketa yasata a mota ya koma gida bemabi takan siyo lemun tsamin ba.... Sai Bayan ya shiga gida yafara tsoron taya zai tinkari mummy dazancennan.. brinta yayi a mota ya shiga falour a zaune ya samu mummy tana jiranshI, Dasauri ta Mike yauwa kasamo kuwa? A'a mum ya tashi da wuri yau, cewa tayi Ayyah kasha wahala sweet heart pls kayi hakuri zan Duba maka d'akin dadunka, jeka kwanta.. Ɗaki Ya shiga ya tsaya a bakin Kopa, saida ya tabbatar mum ta shiga ɗaki sannan ya fita ya ɗaukota yakaita dakinshi, kayanta yagani duk sun baci da kwata kuma duk sun yage.... shiru yayi Yana kallon innocent face dinta, "yanzu ace wannan akebi za'ayiwa fyad'e mtsews God forbid da mugun halin wasu.... rigar ya zare kadan Dayake doguwace, kirjinta yaga ya bayyana, da sauri yace auzubillah, towel ya dauko ya ɗora a saman kirjinta sannan ya zare rigar ta kasa... santala santalan kafafuwanta ne suka bayyana, harya tsaya Yana kallo ya kuma cewa A'uzubillah sannan ya kauda kanshi daga kallonta bathroom ya shiga.. kaya ya cire ya sakinwa kansa showa Yana tunanin rashin imanin wasu... mum ce ta turo kofar, rike da pear guda daya, sarfraz ansamu ɗaya ko manage kayi kafin safiya ko... gani tayi Kamar bashibane kwance... Karasawa tayi, ga mamakinta saitaga Mace ce, ɗaga towel ɗin tayi ganin kyakkyawar budurwa tayi kwance daga ita Sai bra da pant 👙, towel d'in ta gyara ta fita a hankali, koda ta koma ɗaki kasa rintsawa tayi, maiyasa sarfraz zaiyi mana Haka? duk gatan da muka nunamishi ya rasa da abinda zai saka mana saida zina, kuma a cikin gida ma, har yanamin kariyar zaije siyo fruit ashe ita zaije daukowa?.... haka tayita wasiwasi, duk yanda barci ya kware wajen iya sata amma hakanan ya hakura ya kyale idon mummy... koda sarfraz ya fito daga wanka doguwan rigarshi ya dauko a closet ya rufe idonshi ya sa mata, sannan ya Kalli Gefen inda ta bugu da poll wire, be kumburaba Amman Yayi ja sosai kuma kanta yayi zafi..... yanda mummy batayi barciba Haka safraz shima sarfraz kwana yayi gadin yarinyar gashi ko ƙwaƙwaran motsi batayi.. saida asuba ya fita sallah afalour ya hadu da mum yaga idonta Kamar a kumbure " kusa da ita ya karasa mum meya sameki a ido? be wani samu good response daga garetaba hakanan ya kyaleta ya fita zuwa masallaci Bayan Yayi sallar ya koma ɗaki, bathroom ya shiga ya dibo ruwan zafi a basin yasa karamin towel yana danna mata goshinta inda ta bugu a hankali.. numfashinta yaji ya fara fita da sauri da sauri... yana zaune har gurin takwas ya zuba mata ido.... tari yaji tayi tana motsi, da gudu Yayi hanyar falour Don kawo mata ruwa, Karo sukayi da mummy zata shiga d'akin, cewa Yayi mum dama............ bata bari ya gama faɗan abinda zai faɗa ba ta zabga mishi Mari, yana mamaki takuma zabga mishi wani "Hawayene suka zubo daga idonta "safraz duk gatan da muka yimaka Amma ka rasa abinda zaka dawoka saka mana dashi Sai zina, kuma zinar ma a cikin gidan mahaifinka? tunda mukaji matsalar ka mukace zamu yi maka aure amma kakyi yarda.. shine yanzu zaka koma biyebiyen mata. idon safraz yayi ja Yana Kallonta Amma yakasa yin magana jin zargin da mummyn shi keyi mishi Masu karatu kunji abinda ya faru da sarfraz... Shin mummy zata fahimci abinda ya faru kuwa _*MATAR RASHEED*_✍️🎀🎀 SAFRAZ🎀🎀 Episode 7 Written by oum aeyman 💝 Supreme writers association.... We write with the ink of era...... Idon safraz yayi ja, Yana Kallonta amma yakasa magana... Sakamakon wani takaici daya rufeshi "wai ace Kamar shi mummy bata yarda dashiba..... Cewa tayi "wato ka maidani mahaukaciya koh? Inata magana amma kayi banza Dani koh? Wani siririn Hawayene ya zubomai a ido d'aya, "tunani yake azuciyarshi, Dana bar yarinyarnan a wajensu da Allah ne kadai yasan abinda zai faru da ita.... Wai kuma na taimaketa abin kuma ya juya kaina... But I know Allah wouldn't allow this to happen cuz i did it with a good intention..... Mummy ce ta dawo dashi daga tunanin dayakeyi "wato safraz munkai gejin dazan rika yi maka magana kanajina kuma kayi banza Dani koh? Tunda yaji tace safraz yasan ranta Yayi mugun baci, domin bazai iya tuna last data Kira tsuran sunan shiba...... Ahankali ya iya had'a Kalmar "yi hakuri mummy" Murmushin takaici mummy tayi "Hmmm hakuri ya rage naka ai, Yanzu fad'a min a Ina ka daukota? Kuma wacece ita? dakyar safraz yace "bansan taba kuma bansan ko wacece ita ba...... Hanyar d'akin shi mummy tayi "bari ni naje na tambayeta dakaina kaga saitamin bayani..... Sannan ta shige d'akin ..... Nitsewa safraz yayi a cikin sofa, gaba d'aya zuciyarshi na mishi tukuki, saboda baiyi abinda ake tuhumarshi akaiba.... Kuma mai tuhumarma mummy.... Tarar da ita tayi tana yinkurin tashi, da alamu tanajin jiki.... Taimaka mata mum tayi ta Mike.... A Gefen gadon ta zauna ta Dafata "Sannu kinji " Ya jikin naki? A yanayin tsoro nawaz tace "Dan Allah a Ina nake? Cewa tayi kada ki damu babu abinda zai faru dake kinji? D'aga Kai nawaz tayi alamun "to" mummy ce tace zaki iya magana 'yata? Ahankali nawaz tace "eh zan iya" please inaso duk abinda zan tambayeki ki fad'a min gaskiya kinji? nawaz ta d'aga Kai had'e da cewa "to " Mummy ta gyara zama tace "my dear inasone ki fad'a min abinda ya faru Wanda kika Sani a matsayin abinda zaki iya tunawa na karshe.. Nawaz tace to "Amma Dan Allah sammin ruwa nasha! Dasauri Ta Mike ta fita falour tayi dispensing din ruwa a dispenser. sannan ta koma ciki da sauri Mika mata tayi "gashi " Amsa tayi Tasha rabi sannan ta ajiye ragowan a Gefen bed side drawer... Abinda zan iya tunawa shine Daren jiya Na fito daga bayi na shiga d'aki kawai sainaga Maza biyu suna mana dubedube. nace su waye ? Sainaga sun nufoni zasu kamani danaga da gaske ni sukeso su kama shine Nayi Waje da gudu.. Haka Suma suka yi ta bina a baya tundaga layinmu har saida mukakai captain street, sannan ne suka kamani.... Dayan ya rike hannuna da karfi yanda bazan iya kwacewaba, shi kuma Dayan ya Fara yagamin Riga... ganin Dagaske zasu wulakantani yasa na ciji Dayan a hannu, dayaji azaba shine ya sakeni... na juya da gudu naji nayi Karo da wani abu mai karfi to Daganan bazan iya tuna komaiba ..... mum ce tace "ko zaki iya siffantamin kamannin wadanda suka biyoki.. nawaz tace "Eh nasan d'aya ma domin yana zuwa gurin uwar gidan abbana kuma sunanshi Tasiu, Amma bansan Dayan ba, kuma dukansu daka kallesu zaka gane y'an shaye shaye ne...... shiru mum tayi sannan "tace to ke ina mum dinki lokacin da abin ya faru? mamana batanan ta tafi maiduguri a ranar. Sai dai umma kuma koda zantayin ihu bazata kula ni ba..... Mummy ce tace "I'm sorry my dear in a pity face 🤦🏽‍♀..... Wata damuwa ce Mai karfi ta kama mummy domin tasan a yanayin maganar yarinyar babu safraz a ciki kuma batada masaniya ma akanshi , Nayi kuskure Dana dauki mataki banyi kwakwkwaran bincike akaiba! to yanzu me zancewa safraz? Ko taya zan iya kallon shima? Tashi tayi tace wa nawaz bari nazo ƴata! Da sauri nawaz tace, to amma don Allah kafin ki tafi waya kawoni gidannan? Mummy tace "Dana ne ya kawoki, kuma yana falour, haɗe da fita daga ɗakin....... Kallon gadon da take Kai tayi "hmm dagani masu kudine wadannan, domin ji gadon ji closet d'in ma, daga carpet harda yanayin curtains d'in daka kalla kasan masu uban tsadane.... hakadai taci gaba da Kalle Kalle tana wasi wasi... SAFRAZ..... A inda mum tabarshi anan ta tarar dashi Yayi tagumi, wuceshi tayi domin batasan me zata iya ce mishiba..... Bayan mummy ta fita ya mike ya shiga ɗakin. azaune ya tarar da ita a Kan gado tana tunani "tsayawa yayi ya zuba mata ido, domin itama batasan ya shigo ba... "wow! Gaskiya she's very beautiful and charming ... Kalli fuskarta so innocent, da nazo ne na koreta saboda zargin da mummy tayi min akanta Amma na tabbata bazan iyaba... may be Allah just gave me my own crush...... Kusa da ita ya karasa, a gaban gadon ya tsuguna. Charming queen me kike tunanine haka? Firgigit tayi ta kalleshi, wani mamakinne ya daɗa kamata... safraz tagani a gabanta Yana mata murmushi "meya faru? naga ure some how scared, just be calm nothing will happen to you, coz you're safe here Muryarshi da taji yasa ta dada tabbatarwa shine, ga kuma kamshin turarenshi dataji "oud Al azhar" Murmushi tayi mai tace "nagode safraz, wai dama kaine ka kawoni nan? cewa Yayi Eh nine "and please kinsan nine? Sai sannan nawaz ta tuna cewa safraz be taba ganin fuskartaba "sai cewa tayi ai kaima ka sanni koh? A'a wallahi ni bantaba ganinkiba sai dai muryarki is familiar, amma sai dai na kasa tuna inda nasan muryar..... cewa tayi nasanka kuma ka sanni amma Kace baka sanniba.... shikenan tunda bazaki tunamin a inda nasankiba kawai yanzu ki faɗa min wadanda suke binki su waye? Bashi labarin duka abinda ta fadama mummy tayi... shiru safraz yayi "wato dama sun cemin kishiyar mamantace tasasu. Amma kuwa zan musu rashin mutunci wallahi, dago da idonshi Yayi ya zubawa kirjinta ido.... shan jinin jikinta tayi takai hannunta gurin donjin meye, ji tayi rigar ya matseta sosai... Sai sannan ta tuna a yanayin da take "dukunkune hannunta tayi a kirjin ta sauke kanta kasa... karamar wig d'in dake katane ta karasa cirewa , gashin kanta ya baje sakamakon babu kitso a kan.. duk gashin ya rufe mata fuska, Hannu tasa ta kawar da gashin tayi baya dashi, sannan ta haɗa fuska Kamar zatayi kuka "ni Don Allah kadena kallona haka! Ajiyar zuciya sarfraz yayi ya mike ya fita.... a faloun shi ya zauna a Saman center table Yana tunani "meyasa? Nashiga in tambayeta sunan ta kuma in tambayeta abubuwa da yawa Amma na kasa, sai wani cikamin fuska datayi.... Hope kada ta daukeni da wata manufa.... Nawaz....... zaune take a takure tana tuna irin kallon da safraz yayitayi mata "wai dama shi wannan safraz d'in rashin kunyarshi ba iya baki bace? Ji yanda ya zubamin ido, sannan mamakin yanda be ganetaba take, kuma ya akayi ya fita da dare harya kawota gidansu..... sannan dole Yayi rashin kunya masu kudine sosai Ashe..... tana wannan tunanin ya kuma shigowa ya wuceta, closet ya bude wata sky blue ɗin shadda ya ciro Sai daukar ido takeyi, Zanenta Dara Dara "getzner" Sai wani milk ɗin Yadi ya kuma cirowa ya haɗa guri ɗaya ya fita dasu a hannunshi.... be Kalli inda takeba sakamakon yanda yaga ta takure guri ɗaya.... sasan daddy ya shiga Yayi wanka ya shirya, sannan ya dauki shaddar da key d'in Motarshi yabar gidan... A shagon abasu colour yayi parking, cikin shagon ya shiga yana murmushi..... da sauri abasu colour ya taso "oga sarfraz ya akayi baka kirani nazo da kaina... murmushi sarfraz yayi "inani Ina kiran oga mai bamu colours gida, ai Sai a kamani kuma a Hana belina. murmushi abasu colour Yayi "oga sarfraz akwai barkwanci "toya gida ya Al'amura ya makaranta? Lapia lau abasu, dama dinki na kawo urgent inzan samu? Haba oga sarfraz ai kasanma zaka samu.... Wane iri za'a yi maka? murmushi sarfraz yayi "dama daddy ne ya siyomin shaddar nan last week yace amini malinmalin da y'an ciki... to ni kuma na chanza Shawara, inaso adinkamin yadi biyar sauran yadi biyar d'in kuma a dinkawa Wata kanwata. Abasu colour yace ai babu damuwa , sai in dinka maka naka ita kuma Sai dini ya dinka mata, hope kazo da gwajinta? Sarfraz yace Aa banzo dashiba "Amma dai tsahonta Kamar wannan Dana Ke gani a shagon nan kwanaki, Amma saidai gaskiya wannan tafita kirji da kwankwaso..... abasu colours yace Kodai itace madam ɗin? Daria SARFRAZ yayi "Aikuwa kasan abu a duhu cemishi Yayi zai zo ya Amsa da Karfe 3:00pm kudin ya bashi sannan Yayi mishi sallama ya tafi.... Hafab closet ya tsaya ya nemi takalmin couple box ya siya takalman iri daya komai da komai saidai shape d'aya banbanta na Mace Dana miji.. fruit ya tsaya ya siya, sannan ya wuce gida.... 20minutes earlier...... mum naga ta fito daga dakinta rike da gyale ta shiga ɗakin sarfraz, a zaune taganta. daughter na zo muje parlour kici abinci kisha magani koh? nawaz tace to mummy, nagode da kulawar da kikayimin Amma inaso naje gida. to indan wannan ne kada ki damu sarfraz na dawowa Zansa ya kaiki kinji..... Shiru tayi "to Amma dakin bari zanje dakaina. dakyar mum Ta shawo kanta ta yarda akan zata bari ya dawo saiya kaita..... dinning mummy ta jata, sannan ta shiga kitchen ta kwaso warmers d'in abincin da vacuum d'in ruwan zafi.... tea Ta had'a mugs biyu sannan ta zuba mata potatoes wages da fried egg Sai raising bread a gefe ta ajiye a gabanta... ita kuma nawaz mamakin girman parlourn takeyi da uban kudin da'aka kashe kafin a hadashi...... tanaso Ta Kore kwarkwatar ido gashi kuma tanajin nauyin Matar.... ta yi shiru tana wasa da yatsunta taki taci abincin, mummy tace my dear kici mana! Ko inzo inyi feeding dinkine? Dasauri nawaz tace "no thanks zanci yanzu, cup din ta dauka, takai bakinta kenan taji sallamar safraz, Dasauri Ta ajiye a table tayi shiru. Kujerar dake kusa data Nawaz ya ja ya zauna "Barka da safia mum, saboda Sam sarfraz baya iya yin fushi da mummy. Barka safraz, Ina kaje da safennan? mummy naje gurin tailor ne... cewa tayi ok, bari nayi serving dinka, zuba mishi tayi shima ta tura mishi gabanshi... kallon nawaz yayi "mum wannan takici kosaina taimaka na bata? Kallonshi mum tayi "ga mamakinshi yaji tace "to Kila itama irinkace, taimaka kabata sannan ka kaita gida...... gida kuma? Domin ji yayi Kamar ta buga mishi guduma a kirji... mummy tace eh sarfraz ita tace zata tafi.... cewa Yayi to taci abincin tukun, shima ya Fara cin nashi hade da tunanin wace hujja zai kawo wadda zatasa mummy ta hanata tafiya yanzu.... gaba d'aya nawaz a takure take domin Saita faki idansu take ci, kuma idan bataciba sarfraz ya taka mata kafa ta kasan dining, idan takalleshi sai Yayi mata alamu da ido akan taci.... kadan taci tace ita ta koshi, mum tace to my daughter har zaki tafi bansan sunankiba bansan wani cikakken labarinkiba kuma bakibani number wani nakiba balle infada musu cewa su kwantar da hankalinsu kina lafiya.... nawaz ta nuna sarfraz "mummy ai wannan ya sanni. sarfraz yace mummy ni bansan taba..... Cewa tayi shikenan, "mummy sunana Nawaz Muhammad, kuma nice nake musu QUR'AN da fiqhu a HAYATUL ISLAM....... da sauri safraz ya mike Yana nunata "malama Dama kece? wallahi banganekiba... mum tace yazaayi Kace baka gane malamarkaba? mummy bata daɗe da Fara mana karatuba kuma bata taɓa buɗe fuskartaba kullum da niqab take zuwa.. mummy ce tayi murmushi Kace yar tawa ustaziyya ce........ nan safraz ya kwashe yanda yaga Nawaz da masu binta ya fadawa mummy kuma ya Kara da cewa kuma sunce kishiyar mamantace ta turasu gaskiya mum bazata koma gida yanzuba tunda kinga babu Kowa a gidan, kuma zata iya kuma turo wasu su illatata _*Matar Rasheed*_✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 8* *🤳by oum aeyman* Supreme writers association...... We write with the ink of era.... That's era is our ink 🖊 Kuma zata iya turo wasu daban suyi mata illa.... Mum tace hakan Yayi sannan kuma gaskiya ka faɗa saboda yanzu tana cikin riskine.... Nawaz ta shiga tunanin cewa kiyayyar umma har takai ta turo ƴan dabaa su illa tata, Tabbas tasan umma bata ƙaunarta amma bata taɓa tunanin ƙiyayyar takai hakaba.... Safraz ne ya dawo da ita Daga tunanin data keyi "kinji mommy tace bazaki koma bako❓ 😔naji cewar nawaz, saboda ba Haka tasoba..... Mummy tace yanzu yaza ayi da kannenki❓ Charaf SAFRAZ yace mum ai batada kanne ita kadai ce Kamar ni, Murmushi mum tayi "Lallai Ashe dole kacemin kasamu kanwa. To yanzu dai kaje ɗaki ka huta tunda Sai 1:00pm kakeda lecture koh? "Eh mummy amma banajin barci yanzu... nawaz dai kanta na Duke domin a takure take kuma ita da so samune tafison a barta ta tafi gida.... SAFRAZ ne yayi wa mummy signal akan ta Kalli nawaz, Kallonta tayi tace "my daughter meke damunki? Firgigit nawaz tayi "babu komai mummy, dama dai inaso Nayi wanka ne ... Sannan inaso Nayi waya da ummi na.. Mummy tace haba dear, kibari Sai hankali ya kwanta, kada ki kirata ki tayar mata da hankali, idan ta dawo da kaina zanje gidan nayi mata bayani.... Kuma abinda nakeso dake shine ki saki jikinki Kamar kina gida, idan ma kina bukatar wani abu ga yayanki ko dalibinki sai ya siyomiki kinji? Ɗaga Kai nawaz tayi... sannan tace "please inane bathroom d'in? Mummy ce ta rike hannunta,"zo muje na had'a miki ruwan... Mikewa sukayi mummy ta nufi dakinta da ita, a Saman bed ta zaunar da ita sannan ta shiga bathroom d'in. me nawaz zatayi inba kalloba, idanuwa ta baza 👀 tana kallon kayan alatu, hmm masu kudi na abinda sukaga dama, abinda nawaz tace kenan a zuciyarta, domin ganin irin kudin da aka kashewa d'akin. Mum ce ta fito, daughter shiga kiyi wankan na had'a miki ruwan. cewa tayi "nagode mummy "sannan ta Mike ta shiga bayin A bathtub 🛀 taga ta had'a mata ruwan zafi, gashi Sai uban kamshi yake, a gefe kuma ta ajiyemata liquid soap da towel.. ta dad'e a tsaye kafin ta shiga ta Fara wankan, ♾♾♾♾♾ a falour safraz ne zaune Yana tunanin wannan sabon al'amarin! domin ji yake shidai bazai iya rabuwa da nawaz ba, kuma yanajin cewa muddin ya bari ta tafi gida to Lallai bashi ba kuma yin barci, cewa Yayi dama mummy ta roketa akan cewa ta aureni (wayaga Wanda bai Isa aureba kuma yana tunanin ayi mai yanzu) nidai gaskiya nasan son ta nakeyi koda dai ban ta'ba soyayya ba, amma Ai Ina karanta littattafan soyayya kuma Ina kallon movies .. Allah nidai mummy zan fadawa cewa ta fadawa daddy Ina sonta, Mummy ce ta fito ta nufo gurinshi, zama tayi a kujerar dake kallon shi "gyaran murya tayi "safraz Dan Allah kayi hakuri😔 wallahi bada gayya na mareka dazuba... hanata karasa maganar Yayi "haba mummy yanzu aduniyar nan dama akwai abinda zakiyimin ki bani hakuri a kanshi? Mum ta kuma cewa "wallahi safraz akwai domin na zalunceka kuma na maka kazafi saboda na zargeka akan abinda bakayiba kuma na.......... Hannunshi ya d'ora a Saman bakinta "mum keep quite pls, i don't want you to say a word again about what have been a past now... Ni wallahi banji haushi ba, saboda laipinane daban fad'a mikiba kuma abinda kikayi, haka kowace uwa ya dace tayi hardai tanason danta ya zama na gari.... abinda yasa kuma ban fad'a miki da darenba, tsorone kuma banaso dad yasani... Amma Insha Allah zan kiyaye gaba kuma kiyi hakuri bacin ran Dana saki..... kukane ya subce wa mum domin irin maganganun da safraz ya fad'a mata sun kara tabbatar mata da irin tsantsar kaunar daya Ke yimata... amma gashi ita harta zargeshi, kenan yafi sonta? Mikewa safraz yayi ya rungumeta "Dan Allah mum kidena, banaso... goge Kwallar tayi sannan Yayi shiru tana Duba irin Hakurin safraz.... Zama Yayi kusa da ita Yana cewa "ko kefa mum? Dazuma Ina kallo ko abincinma baki wani ci Dayawa ba.... D'iba Yayi a spoon ya nufo bakinta dashi "mum bud'e in Kara miki kadan domin nasan baki koshiba..... Murmushi tayi ta bud'e bakin.... ♾♾♾♾♾♾♾ umma nagani zaune ta doka uban Tagumi domin Tasiu ya kirata ya bata labarin cewa wani ya taimaki nawaz.. sannan ya shaida mata abokin aikin nashi ma 'kashin hannunshi ya goce, Shikuma Yana fama da wani irin azababben ciwon Kai saka makon gusumar da mutumin ya buga Mai... Waya ta dauka ta Kira fauziyya ta shaida mata cewa Maza Maza tazo akwai Matsala .... ko mintuna goma ba'a yiba sai ga fauziyya... nan umma ta zauna ta zayyanemata abinda ya faru. shiru fauziyya tayi "to umma yanzu yaza ayi? fauziyya wannan abin bafa karamin abu bane domin idan nawaz ta dawo zasu fadawa y'an sanda. kuma nawaz zata fad'a cewa akwai Tasiu, kuma kinga idan Tasiu yaji duka zai iya fad'a cewa Nina turasu.... fauziyya tace "umma aini nasone kisa Wanda bata saniba.. Gashi yanzu kinga abinda ya Faru.... umma tace na shiga uku kada asirina ya tonu! Fauziyya tace "abinda za'a yi yanzu shine ki shirya mu tafi gurin boka mufada mishi abinda ya faru, kinga in akwai abinda zaiyi ya kulle bakinta ta kasa fad'a aikinga mun samu sauki ko? Umma harda yin wani shu'umin murmushi domin tasamu mafita.... agurguje suka shirya suka dau hanya... ♾♾♾♾♾♾♾ nawaz ta fito daga wanka, tarar da Wata sabuwar doguwar Riga orange colour da veil dinta a gefen gado... Sannan kuma harda kayan make'up Sababbi.. lotion tadan shafa kadan tasa powder, sannan tasa matte lipstick 💄 tadansa kohl da eye liner.. Rigar ta d'aga zata sa, ga mamakinta saiga bra harda pant Sababbi a kasan rigar.. shiru tayi daga bisani ta dauka tasa, sannan ta d'ora rigan a sama... wow! What an amazing lady? dai dai rigar tayi mata, Kamar an gwadata... Mirror ta karasa ta dauki comb tadan taje kanta sannan ta tufkeshi, Veil d'in tayi Rollin a kanta sannan ta dauki wani turare hayaa tadan fesa... rasa yanda zatayi da nata bra da pant din tayi, yanke Shawara tayi ta kaisu bathroom ta wanke tayi hanging.... Parlour ta fito a hankali domin nauyin mummy takeji.... Safraz da fuskarshi take santar kopar mummy, tana fitowa ya zuba mata ido Kamar Dan kauye yazo binni .. ta lura da irin kallon daya Ke yi mata Amma Saita basar... bataje dinning ba Saita zauna a couch dake tsakiyan faloun.... tashi Yayi ya koma kusa da ita, "harkin shirya? Murmushi tayi "Eh safraz nashirya, ina mummy? mummy tana kitchen zata dora mana lunch, kinsan ita tace batason y'an aiki wai itama yar aikin kantace.. Murmushi nawaz ta kuma yi "ai tanada gaskiya gara tayi abinta da kanta ta samu lada sannan nagama ai bakwada wani yawa. Safraz yace eh bamada yawa, Daga ni Sai dad da mum da maiba garden ruwa Sai driver, yanzu kuma kinga mun karu koh? murmushi tayi "nida zan koma gidanmu, ai bandani... ji yayi Kamar ta zuba mishi ruwan zafi a zuciya... barin yanda kayan suka Kara mata wani irin kyau kasancewarsu orange ga kuma fuskarta dayaga hartafi da yi mishi kyau.... Cewa Yayi "hmm kinzo kenan dankiji! yar siririyar dariya tayi "to shikenan bari na je na taya ummi Au mummy girki... Mikewa Tayi ta nufi inda take zaton nanne kitchen d'in.... bin bayanta Yayi da kallo, Hip dinta na juyawa a hankali Kamar dakanta takeyi, sannan tana tafiya a sanyaye... cewa Yayi wallahi bazai yuwuba, nasan gidansu akwai Maza. kenan haka Suma suke Kallonta? Mikewa Yayi yabi bayanta, tarar da ita yayi Tana cewa "Allah mummy kibari zanyi, mum tace "to shikenan yanzu ni ki dafamin farar shinkafa da beef stew, ku kuma saiku dafa duk abinda kuke so... safraz ne yace " to mum we will do as you said.... da sauri ya bud'e fridge ya dauko freeze beef da freeze chicken, Murmushi mummy tayi "to agama Lapia, sannan ta juya Ta tafi. kunna gas nawaz tayi ta dora tukunyar akan wuta sannan ta zuba naman a ciki Bayan ta wanke.... albasa ta yanka akai ta zuba curry da sauran seasoning da spicies ... d'aya gas d'in ta kunna sannan ta d'ora sanwar ruwan shinkafar... Maggi safraz ya dauko, guda nawa zan bare? "10"tace a takaice, haka Yayi tajan ta da hira har saida ya samu ta saki ranta.. har saida suka koma suna rigerigen zuba abu, gurin sauri nawaz a Kai hannu tukunya ta kone, Dasauri safraz ya kama hannun Yana firfitawa sai faman Sannu yake mata. Amsar hannunta tayi gami da cewa kadan ne pah.. Misalin 11:43am sun gama abincin, warmers safraz ya kwaso ya kaiwa nawaz ta jujjuye a ciki, mum anyi mata rice and beef stew d'in datace, su kuma tayi musu chicken biryani. wanke Hannu tayi a dish washer na kitchen d'in sannan ta goge fuskar ta.... warmers d'in suka kwasa zuwa dining suka jera... kallon safraz tayi "Dan Allah inaso nayi barci, ko kadan ne?! murmushi yayi "to kije ki kwanta mana, cewa tayi ai bansan inda zan kwantaba.. cewa Yayi kije d'akin da kika kwana, d'akin safraz ta nufa ta shiga, a falour Ta kwanta Saman three sitters couch.... tana kwantawa barci yayi awon gaba da ita. Bayan Kamar minti goma safraz ya shiga d'akin, ganinta Yayi kwance tana barcinta peacefully. Karasawa yayi Yana Kallonta, "datasan dakinane nasan bazata yarda ta shigoba balle harta yi barci a cikiba. murmushi ya kuma yi "kalleta Mai kyau Dan Allah... zama yayi ya zuba mata ido yanata kallo, ita kuma Sai barcinta takeyi hankali kwance motsi yaga tayi, da sauri ya tashi, . cigaba da barcinta tayi Shikuma ya zauna yana tunanin me zaiwa wadanda sukaso ketawa malamarsa haddi.. anan shima barci ya daukeshi..... ♾♾♾♾♾♾♾♾ umma nagani zaune gaban wani farin tsoho fuskarshi duk buyagin gemu. fauziyya ce tayiwa bokan bayanin komai sannan tace suna sone a rufewa Nawaz baki yanda bazata iya fadan komai a kaiba Nan bokan yadanyi siddabarunshi yace komai ya kammala. godia sukayi mai sannan umma ta ciro kudi ta ajiye a gabanta sannan suka tashi suka fita... saida sukayi tafiya mai Nisa sannan suka Isa titi, kasan cewar a sabuwar unguwa gidan bokan yake.. gida suka koma suna farin cikin anrufe bakin Nawaz (inba bata ba ace wani Wanda bai iya yiwa kanshi abubane zai iya yi maka, kana zaune a gurin yayi shirme Amma ka yarda ♾♾♾♾♾♾♾♾ sai wurin karfe 1:25pm mummy ta tashi daga barci, kitchen ta duba bataga Nawaz ba sannan duka dakunan gidan ta duba Amma batanan. d'akin sarfraz ta tura ta shiga, "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un mummy tace ganin....... please nagaji kuyimin afuwa... *OUMMOU MUHSIEN* 😍*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 9* ✍🏻 by oum aeyman Supreme writers association.... Ganin sarfraz Hankalinshi kwance yanata faman barci...... Hancinshi ta matse iska ta daina shiga, Dasauri ya bud'e ido ya tashi...... Mitstsike idonshi Yayi sannan yace mummy kin tashi ashe😳 Mum tace "ban tashiba Kai yakamata in tambaya koka tashi? Murmushi yayi "mum menayi kuma? Cewa tayi "kazauna tambayata Bayan kacemin 1:00pm kakeda lecture kuma gashi yanzu 1:30pm Kayi sauri ka tashi ka shirya, kasamu kaci abincin ko kadanne saika tafi.... Cewa Yayi to mum, sannan ya fita. Juyawar da Mum zatayi kawai ta hango nawaz sai faman barci takeyi, duk ta saki jiki.. Karasawa tayi tad'an tasheta kad'an, bud'e ido tayi suka had'a ido da mum, da sauri ta tashi domin Sam ta manta ba'a gida takeba..... Mum tace meyasa kikazo d'akin safraz? Maimakon kizo nawa, inma bakyason nawa ai akwai d'akuna da yawa.... Cewa tayi d'akin sarfraz 😳❓ mummy wallahi bansan d'akin shi bane 🤨. Kuma aishi yace nazo nan😔 "kada ki damu my dear ☺, nasan halin sarfraz zaiyi fiye da hakama. yanzu kizo muje kici abinci kiyi sallah koh? "to" tace sannan ta Mike tabi Bayan mummy. A dining suka tarar da sarfraz har Yayi serving dinsu, mummy ta balla mishi Harara "wayace maka yanzu zamuci daka wani zuba mana ❓ cewa Yayi ai nafiso taci da wuri saboda mu tafi da wuri kada na rasa lecture na🤨.. Mum tace ban gane ku tafiba 🤔 cewa Yayi "dama dazu da Muna girkine tacemin Dan Allah idan zan tafi makaranta zata bini in siyan mata kayan kwalliya da hijab shine nace mata to. kallon nawaz yayi "koh malama 😋😉❓ ☹ 'bata rai nawaz tayi "yaushe nace maka haka 😟? fuskar mamaki sarfraz yayi "haba malama fisbilillahi Don kinajin kunyar mum saiki chanza magana 😉😎 Cewa tayi "Allah niban ce maka hakaba 😡 mum tace "shikenan yi sauri kici abincin kiyi sallah kibishi kada ya rigaki, "Mum Allah niban ce mishi hakaba 😦 mummy tace " shikenan, koda bakiceba tunda Yayi niyyah saikije ya siyan miki d'in, yi sauri my daughter ☺ nawaz ta cika tayi bam ji take Kamar ta zabga ihu, Shiko sarfraz murna fal cikinshi..... bini bini ya kalleta Yayi mata gwalo 😛😋😜... sunkuyar dakai tayi takicin abincin, mum ce ta ta'ba ta "my daughter kici abincin mana! Charaf sarfraz yace "mum tun dazu tacemin Idan muka fita in siya mata ice-cream 🍦 da chocolate 🍫, wai su take sha'awa yau... OK "tunda bakyajin cin abincin to yi sauri kije kiyi sallah kafin ya gama..... Tashi tayi ta nufin d'akin mum, Tana shiga tace "wayyoo oh ooo 🤯 wai me wannan sarfraz d'in yake nema danine ❓ ya daukeni tamkar sa'ar shi, to kuwa zan koya mishi hankali, wallahi donma Ina jin kunyar mummyn shine..... Bathroom ta shiga donyin alwala, amma me? Jikinta ta gani a 'bace, cewa tayi na shiga uku, baka kyautamin ba coz bakazo a lokacin daya daceba... inani inayin menses a gidan mutane, mutanenma irin sarfraz ❓ cire pant d'in Tayi ta wanke, sannan ta dauki tsohon nata data cire ta mayar.... gyara fuskarta tayi, sannan ta fita falour... "yauwa malama kin fito a daidai nima na gama. murmushin ya'ke tayi sannan tace hmm, wani sabon flat shoe mum ta mika mata "kisa wannan koh! Murmushi tayi "nagode mummy, Mum tace "you don't have to, and kuma batun hijab zaki zauna a mota saiya amso miki kisa koh? murmushi ta kumayi ''to mummy " to to Kuyi sauri kunga har biyu tayi, har parking lot ta rakasu sannan ta koma d'aki,, Suna fita daga gidan sarfraz ya kwashe da dariya 🤣😂🤣😂😂🤣😅"ya kikaga salon nawa? Harararshi tayi ''wallahi kaima zakazo Hannu, saboda kasan mum zata goyi bayanka shine kaketa yin karya kana jonawa Dani koh? malam saukeni anan 🤨.... Hmmm ki sauka mana, kinga saiki tanadarwa mummy Amsar tambayoyin dazata miki Idan kika koma😎 domin a gabanki tace asiyo kayan da yawa kuma itama tace na siyo mata grapes 🍇... balla mai Harara ta kumayi "naga alamun kama manta ni malmarkace koh? kashe mata ido Yayi 😉"kin manta ni kuma yayankine koh❓ enough!!!!!! 😡😡😡😡 daga yau nafasa y'an uwantakar, ko dolene? "calm down little sister nasan Rankine ya baci, Amma dazaran kinsha ice-cream you will be alright.... 😇 banza tayi dashi batace komaiba,, , baiji dad'in shirun data yiba domin yafiso ta tayashi suyi tayi ... a classic boutique yayi parking, cewa Yayi tsaya inzo, kada pa ki fito a haka.. ... kauda kanta tayi gefe "alamun batajin abinda yake cewa cikin boutique d'in ya shiga, Kamar 13mins saigashi ya fito rikeda Manyan shopping bags 🛍.. . motan ya shiga ya d'ora duka kayan a cinyar nawaz sannan ya Fara driving. Hanyar kasuwa taga yayi ba hanyar school ba, cewa tayi "sarfraz makarantarfa? Ko so Kake karasa lectures? murmushi yayi "nifa yau banada lecture, dama saboda inzo gidanku nayi wa mum karya, kuma saigaki Allah ya kawomin Ke a sadaka.. . "hmm 'karya dai haramun ce kuma Ina kyautata zaton tun kana yaro kasan haka! "Nasani Amma saiki Duba dalilin yin karyar tawa, inasone naje naga kanwata kuma hakanan freely bazai yuwuba.. .. Harararshi nawaz tayi sannan tace "okay fine do what ever you like! fresh vitamins Yayi parking, cewa Yayi ''zo muje tare, da gayya ta Mike zata fita Haka kodon taji me zai ce mata, da sauri yace "kiduba jakunkunan akwai hijab kisa kafin ki fito, yaza ayi ki fito haka? dariya tayi aranta sannan ta koma tasa hijab d'in , tana fitowa mai stall d'in yace hajjaju me za'a zuba miki? Harara sarfraz ya balla mishi "malam concentrate on me not her, "Ke kuma koma mota. ... zuba mini pomegranate da pear da apple da grapes da banana da lime da lemon da kuma pineapple and watermelon.. ... Polythene bags ya dauko yanata packaging dinsu da sauri.. . Sannan ya mikawa sarfraz, yayi service dinshi ya shiga mota. .... malama kinga mutum yanata kallonki, aiya kamata ki koma dakanki kafin wani yace miki Banza tayi dashi, domin abin nashi ya Fara bata tsoro, saikace wani mijinta sahad stores ya wuce da ita nanma hanata fita tayi.. ai kuwa Yana fita taga chanji a cikin bags d'in kayan, waje Ta leka ko zata hango Wanda zata aika, wani saurayi ta hango zaune kusa da exit. fita tayi kusa dashi "Barka dai Dan uwa, "Barka hajiya... Dan Allah kozaka taimaka ka samomin yaro nadan aikeshi ciki? dariya yayi, hajiya ki aikeni mana! murmushi Nawaz tayi "habadai da girmanka? Allah ki aikeni wallahi ni dako ma nakeyi anan ,,, d'ari bakwai ta mika mishi, "Dan Allah ka shiga ciki ka siyomin always pad, idanma baka ganeba zaka iya cewa abaka pad, saika ri'ke sauran chanjin,.. cewa Yayi hajiya nagode, sannan ya tafi tana tsaye a gurin Bayan minti Kamar hudu saigashi ya fito rikeda karamar bakar Leda "hajiya gashi Amsa tayi "nagode Dan uwa na, tajuya zata tafi da sauri yace "hajiya chanjin pah? murmushi tayi mai "babu komai ainice nace ka rike, kwandonshi dake jingine a gefe ya dauka, nagode kingama gida zani domin wani zubin Sai in yini anan amma dakyar zan samu d'ari biyu Sai dai in Allah ya hadani da irinku.... murmushi tayi mai "to shikenan ka gaida gida nagode, har tana Daga mai hannu.. duk abinda ake sarfraz na gani, da sauri ya tawo Amma sai dai kafin ya karaso ya riga ya tsallaka titi.. jiyayi Kamar ya zabgawa nawaz Mari, "who the hell are you, nace ki zauna a mota shine kika fito? tukunama waye wancan d'in? cewa tayi "ya birgenine shine na fito mu gaisa,. kam bala'i, wallahi bazai yuwuba idan na karyashi sai Inga ta inda zai fito daga gida balle kiganshi harya birgeki... hanyar titin yayi zai tsallaka, da sauri ta rike rigarshi ta baya... "yi hakuri kada ka bigi Dan mutane wallahi aikenshi Nayi.... nan fad'an ya koma kanta, meyasa zaki aiki wani Bayan nima ciki na shiga, Fige ledar hannunta yayi yayi wurgi da ita, baza'a yi amfani da koma meye ya siyomiki ba.... bud'e baki yayi Yana kallon always pad d'in data fado daga ledar... dawo da kallon shi yayi gareta, ita kuma ta dukar dakai.. wato kin yarda wani bare daban ya siyomiki pad da ki fadamin na siyo miki koh? duk kunya ta kamata "nifa ba Haka bane, kawai mu tafi gida Dan Allah... ya gane kunya ta kamata, kawai Sai yayi shiru sannan ya koma cikin store d'in, Wanine ya tawo rikeda kayan daya siya, Shikuma a hannunshi ya riko Babban pack din great lady pad me 75 piece... baya ya bud'e aka zuba duka kayan sannan ya bud'e mata, shima ya koma driver side ya shiga.... gurin abasu colour ya wuce, anan ya Amsar musu Ɗinkin shaddarsu .. sai around 3:00pm Ya koma gida kayan duka ya kwasa yakai dakinshi ita kuma ya bata ledar shaddar ta yace taje Ta shirya... a d'akin mummy tayi wanka sannan ta bud'e ledar Dan shiryawa. shadda tagani light blue da hijab blue black Sai takalmin shima blue black, da pant dozen d'aya Sai great lady pad ɗin shima a ciki shiryawa tayi ta fito, a parlour ta tarar da sarfraz shima ya shirya... mum ce tace "sweetheart yau kun taso da wuri,, Nawaz tace Dayake malamin nasu Bai wani dad'e a hall dinba... abincin Suka kara kadan sannan sukayiwa mum sallama suka tafi "dama yau kinyiwa y'an ajinmu alkawarin zakizo babu niqab koh? to amma ki Sani Daga yau babu Ke babu kuma zuwa babu niqab.. Ina ruwanka! tukunama waikai ubanane ko mijina? murmushi yayi mata waya sani abu a duhu..... tunda yace Haka bata kuma maganaba saida aka Karasa islamiyyar... ko kyakyawan parking bata bari yayiba ta fita daga motar, stairs ta hau ya karasa ajin amma babu Kowa saka makon sunzo da wuri, a sit dinta ta zauna sai jinta tayi a kasa warwas, tashi tayi ta zauna a sit dinsu sarfraz, tana mamakin Wanda Yayi mata tarko donya bata kunya a gaban dalibanta... Bayan Kamar minti....... *MATAR RASHEED CE✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 10* ✍🏻 *Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji* Supreme writers association........ Bayan Kamar minti uku da faɗuwar Nawaz, sarfraz ne ya shigo... "malama munzo da wuri kinga babu Wanda yazo ma ☺... Cewa tayi ai gara da muka zo da wuri, wallahi yau danasha kunyar daban ta'ba shantaba..... "meya faru my sister? Cewar sarfraz cikin rudewa "wani aka samu ya karya kujerar nan sannan ya maida ita ya jogana, ina Hawa saijina Nayi a kasa warwas, kuma gashi dama cikina Yana min ciwo........ Fam SARFRAZ ya kumbura domin yasan tarko y'an ajin suka hada mata domin kwana biyu basa ganin fuska ta gurinshi....... Fita yayi daga Ajin baiko bata amsaba, sakamakon jinshi da yake dazai kama Wanda yayi wannan abun mai rabasu sai Allah...... Nawaz na zaune a aji har sama da minti ishirin, Abdul taga ya shigo Ajin.. Binta yayi da kallo ya kasa kauda kanshi har zancen zuci yafara "ooh sabuwar zuwa muka samu kenan? Itakuwa wannan Daga Ina? Wallahi na samu budurwa, garama Nayi Maza na sanar da SARFRAZ tunkan yazo ya ganta yayimin fin karfi.... Ahankali yace "Sannu " D'aga mishi Kai kawai tayi domin har yanzu fushi take, Fita daga Ajin Yayi yana dad'a Kallonta "Anya wannan bayar India bace, naga koda namata magana d'aga Kai kawai tayi alamun batajin Hausa.... Ahankali y'an ajin keta taruwa ,amma duk Wanda ya shigo saiya fita.... "duk abinda sukeyi Nawaz na kallonsu, cewa tayi "yau kuma wani sabon iskancin suka fito dashi kenan, Zadai mu gani Su Mariya sai lekenta suke domin duk Wanda yazo Sai abdul ya tsayar dashi yacemai ya leka aji yaga budurwarshi... dai dai nan sarfraz ya karaso, Abdul ne ya tsayar dashi "SARFRAZ good news, tsayawa sarfraz yayi domin a tunaninshi zancen kujerar da aka karya zai mai..... "ka shiga ajinmu zakaga Wata zaune a seat dinmu, budurwata ce amma yau tafara zuwa..... Mamakine ya kama sarfraz domin yasan nawaz ce zaune a seat dinsu...... Ajin ya shiga Tabbas Abdul ya maidani wawa "zaici Kut*mar ub*nshi wallahi hardai ya Kara had'a Nawaz dashi" dai dai ita ya karasa "malama kiyi hakuri, naje na fadawa malam bilal kuma wallahi ranshi yayi mugun baci domin naji yace duka Ajin zai Zane.... 😳fito da ido Nawaz tayi "harda Kai kenan? murmushi yayi "calm down, banda ni saboda aini naje na faɗa mishi... Sai sannan Nawaz taji dad'i aranta, domin tasan ba sarfraz bane Yayi saboda through out suna tare..... QUR'AN d'in SARFRAZ ta Amsa sannan tace yace yan ajin su shigo insun shirya, fita yayi "malama tace ku shigo inkun shirya? "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un suka had'a ba'ki "wallahi bamusan sanda malama Ta wuceba..... tsaye sukaga yarinyar da Abdul yace budurwar shice, rikeda QUR'AN din sarfraz, domin QURAN dinshi dabanne Kusan duka yan Ajin sun San shi..... "ku bud'e zan fara" cewar malama Nawaz tana dad'a maida hankalinta kan QUR'AN d'in hannunta..... duk yan Ajin suman zaune sukayi domin sun gane malama Nawaz ce daga yanayin muryarta da salon maganarta 😳🤔😱 nan Abdul ya Fara zancen zuci, domin Sam ya manta jiya malama tace zatazo babu niqab.... Kallonsu tayi "waiku me kuke bukatane? Idan bakwason karatun ku fad'a min sai in tafi gida.... kasa bata Amsa sukayi, matan addu'a suke aransu dama sune masu kyanta, su kuwa mazan cewa suke dama zata yarda Ta auresu.... ganin sun zuba mata ido basu ce komai ba yasa tayi hanyar Waje, saboda dama idan tana period tacika saurin fushi da damuwa..... jikin wani ta fada, saura kiris su fad'a Saman stairs, sarfraz ne yayi saurin janye malama naywaz daga jikin malam bilal Wanda ya zuba mata ido.. Don Allah malam kayi hakuri " cewar Nawaz tana kallon malam bilal... charaf sarfraz yace ai babu komai domin yasan y'an ajinne suka bata miki rai... bilal ne yace wannan ce malama nawaz, aikuwa zan nemi gurin shiga zuciyarta domin yan ajinnan sun banu yau kodon na farantamata Kila na birgeta Dalilin haka.... Duk a zuciya yake wannan zancen zucin cewa Yayi habadai ai babu komai.... SARFRAZ ji yayi duk haushin malam bilal ya kamashi saboda ya lurada yanda yake kallon Nawaz sannan dad'in dadawa ta fada jikinshi.... cewa Yayi malama mu tafi gida kawai, kasa suka sauka..... mota ya bud'e mata ta shiga sannan shima ya shiga side dinshi ya tuka suka fita daga makarantar........ LA LA LALA LALA..... MALAM BILAL DA YAN IBN KHATHEER 🥳 Kowa yasa guiwarsa a kasa! nan jikin Ƴan ajin yahau rawa saboda dama tunda sukaga malam bilal a Ajin sukasan yau sun shiga dari so d'ari.... Saboda malam Bilal yayi ƙaurin suna wajen duka..... Abdul ya nuna "fito ka bani hannunka idan kuma ajiki kakeso to duk daya.... jikinshi na rawa ya fito "malam don Allah kayimin a hannu" Dariya bilal yayi saboda tsabar tsoron daya gani a cikin idon Abdul... "to tunda Kace a hannu za'a yi maka, ko arbain da tara nayi ka kauda hannunka to wallahi duka ta zube saina fara daga farko..... nan Matan Ajin sukaji Kamar su saki fitsari a wando jin bulala hamsin za'a yi musu...... gashi a dokar bilal ba'a bashi hakuri saboda Idan aka bashi hakuri kara yawan bulalarma zaiyi.... hannu Abdul ya mika mishi aranshi yanata faman cewa Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un... wani irin shoking yaji ya ziyarci duka gabobin jikinshi... Haka Yayi ta daurewa har akayi ishirin da bakwai, wasu har sun Fara kuka ganin dukan yake Dagaske.... Azabace tayiwa Abdul yawa, baisan sanda ya kauda hannunba.... dariya bilal ya kyalkyale da ita, kash yanzu kadawo Dani baya.... dukanshi ya farayi ta Ko ina a jikinshi Kamar wankan jego, saida yayi mishi bulala hamsin da biyar sannan ya tsaya "bulala biyar d'in dana kara maka ta dawo Dani baya dakayine.... Ko motsin kirki Abdul ya kasa, nagaba ya fito cewar bilal daukeda murmushi a fuskarshi...... Kowa kasa fitowa Yayi yana fargabar yanda zasu kare, bilal ne yace na kara bulala goma akai yazama sittin kenan kuma idan kuka bari na biyoku to wallahi kun shiga dubu..... still babu Wanda ya iya karfin halin fitowa..... bencin su zainab ya karasa, kamata yayi ya tattare hijab dinta, tunda ya Fara dukanta saida ya yimata bulala tamanin ya tsaya, tun tana kukan har saida ta shiɗe ta kasa saidai jikinta da keta faman rawa... Haka ya kama usman shima chasain, duk Wanda ya kama saiya karamai bulala goma akan Wanda ya gama.... kan shatu akazo 🤩😜 daya riketa naji yace dama kwana biyu Bana ganinki a group d'in oum aeyman novels,,,, Cikin rawar murya tace wallahi malam Banida data ne amma Dan Allah kayimin hakuri.... Dariya yayi kawai sannan ya Fara zuga mata bulala, jinayi tana Affiah, marina, Maria, sister saudat, Dr masoud, Dr Bashir, sadauki, Fateema, abbba, Aliyu Hero, oum aeyman dadai sauransu Dan Allah kuzo ku taimakamin...... nida nake labe Ina kwaso muku jawabai cewa nayi maigidan zazezagi ya shiga, ai ban ankaraba saiki nayi sadauki ya tura Dr Bashir, bilal ne ya zuga mishi bulala d'aya "kai me ya kawoka ajinnan inace a IBN TAIMIYYA kake Da gudu Bashir ya fita, still ji nayi an tura Marina, ganin marina nayi Kamar tsunsuwa tayi wuf Ta dire ta window... tsaye nake Ina dariya naji Kamar MARIYA zata turani nima, Aida gudu na fita daga makarantar nabi su sarfraz domin nasan ko bulala daya akamin sainafi Wata banyi typing da posting ba..... a gate d'in naci Karo da saudat Besty tana tambayata ko naga shatu "Kishiga ciki kiga" Domin bansan yin magana mai tsawo,... mai purewater na hango Yana tafe, tsayawa nayi insiya daya indansha kafin na karasa gurinsu sarfraz bula ruwan keda wuya naji an hankade ruwan nima anyi gaba Dani, kafin in dago na kumajin anyi gaba Dani, dagowar dazanyi na hango bilal biye da ABBA mai gidan zage zagi Yana zulamai bulala a baya, Ashe shatu da bestyne suka hankadeni. ai bansan sanda Nayi wurgi da wayar Tawaba nima na ari ta kare, Pls 🤣🤣😂😅😅😂 KUYIMIN ADDU'A ALLAH YASA WAYAR BATA FASHEBA, SABODA IDAN TA FASHE BANI BA KUMAYIN TYPING HARSAIKUN HADA KUDI KUN SAIMUN SABUWA *OUM AEYMAN CE✍️....**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 11* ✍🏻OUM AEYMAN Supreme writers association...... We write with the ink of era....... Su SAFRAZ nabi Don ganin wace wainar suke toyawa..... A mota nagansu zaune SARFRAZ yayi parking a Gefen titi "haba malama! You should treat me like a brother.... Ace kina cikin damuwa ki'ki fadamin meke damunki? Aiya kamata ki fad'a min tundazu fa nake ta tambayarki.... Murmushin ya'ke tayi "SARFRAZ tunda nace maka babu komai ya kamata ka yarda, kawai dai banajin dadine..... "to shikenan in kaiki Rosario park? "eh tace domin batason ta gwaleshi da yawa.... Murmushin jin dad'i Yayi jin cewa ta amince "to mutafi kenan koh? "Eh Amma Don Allah kada mu dad'e domin inaso ka kaini gida saboda akwai kayan danakeso na dauko kuma bayannan wayarka da tawa.... 'bata fuska sarfraz yayi "haba sister nidai kibar zancen zuwa gidannan kawai.... I promise you bazan dad'e ba.... "aini ba dad'e warki bace damuwata, kawae Ina tsoro kada muguwarnan ta kara cutar dake ne.. Murmushi tayi "haba aini nasan babu abinda zata iyamin balle gakama ☺ Sarfraz yaji wani dad'i aranshi ganin nawaz tayi relying akanshi..... Reverse d'in motar yayi zuwa hanyar gidan su Nawaz... yan mintoci ne yakaisu, parking yayi "madam Mun iso 🥰 Murmushi tayi "okay nagode bari na shiga yanzu zan fito Insha Allah.... Sannan ta bud'e motar tafita zuwa zauren gidan. tsaye SARFRAZ yayi Amma sai yaji Sam zuciyarshi bata kwanta mishi akan ya barta ita kadai ta shiga ba ...... bin bayanta Yayi, tsakar gidan ya kalla kopopi yagani guda Hudu kuma ya kasa gane waccece tasu Nawaz... Da bangon zauren ya jingina Yana Kallon ta inda ntawaz zata fito..... ita kuma Nawaz tana d'aki domin kopar dakin ma a bud'e ta ganta gashi duk anyi musu kaca kaca da wardrobe da drawer... Mamaki take to waye yayi haka, kuma me suke nema? Da sauri ta Duba inda ta ajiye wayar SARFRAZ, ajiyar zuciya tayi domin tazata an dauke. Parcel d'in ta duba shima bataga an dauki komai a cikiba.... tunani ta Fara domin ta rasa me aka dauka a d'akin... wayarta Ta nema Ta rasa, babu inda bata dubaba Amma babu ita babu ala munta.... zama tayi a Gefen gado tana tunanin me kuma aka shirya mata dayasa aka daukar mata waya.... SARFRAZ dake tsaye a jikin zaure, umma ya gani ta fito daga wani d'aki Ta shiga wani.... zancen zuci ya Fara "ko wannan ce ummar to wane d'aki Ta shiga kuma? bin bayanta yayi domin Sam yaki samun natsuwa a cikin zuciyarshi... sama sama yake jiyo fad'a "wato natwaz saboda mahaifiyarki batanan shine kika ƙi kwana a gida ko? Salon ki kwaso cikin Shege ace nice ban kula dakebako? "haba umma wai meyasa kullum Ke bakya ta'ba min Fatan Alkhairi ne? Yanzu umma ninayi miki kama da yar iska? "kwarai kuwa kinyi domin, ko ba'a fad'a ba mutum yaji shekarunki kuma yaji bakiyi aureba sannan Bakida niyyar yi ai dole yasan Maza gareki a Waje ...... kuma wallahi zakisha mamakina domin naci alwashin saina ruguzaku keda uwarki, sannan yauma nasan tunda baki fitaba Kila ki Kira kwarton naki yazo nan, abinda zan fad'a miki shine a dai daure asa condom..... saukar Mari taji a fuskarta Wanda tunda take bata ta'ba jin irinshiba..... kafin Ta gama mamakin waye ya mareta ta kuma jin wani Wanda yafi na farkon azaba..... "ita kanta Nawaz sumar tsaye tayi ganin SARFRAZ idonshi Yayi ja Sai wani irin numfarfashi yakeyi.... umma kuwa dakyar ta iya bud'e ido "Nawaz ni kika mara? SARFRAZ ta gani tsaye, kafin takai ga tantanceshi ya kuma sauke mata wani tafin.... "SARFRAZ ya Isa haka! Tukunama wayace ka shigo gidan nan? kobi takanta SARFRAZ baiyiba ya karasa gaban umma " Ke tsohuwar banza, wato bazaki hakuraba kenan ko? kin tasa yarinya a gaba sannan kin hanata sukuni Bayan haka lapiyar da Allah ya batama ba'kin ciki kikeyi, to bari kiji wallahi Nawaz tafi karfinki da ikon Allah.... sannan ki sani cewa ko trailers zaki turo ta Maza akan suyiwa Nawaz fyad'e wallahi bazasu ta'ba samun nasaraba insha Allah, domin ita batada hakkin ki..... abinda nakeso ki gane shine "Nawaz dai dai take da mata d'ari a gurina.... umma ce tace "dama mana tunda tana baka jiki abanza ai dole Kace haka kuma b.......... bata karasa fad'a ba taji saukar Mari, wani ya kuma wanka mata daidai ya jera mata biyar a tare sannan yace "cigaba da fad'an abinda kike fad'a...... kukane ya kamata, ganin anacin mutuncinta domin bata ta'ba zaton hakaba.... Jinine ya Fara zuba a bakinta, ...... nunata da yatsa SAFtRAZ yayi "zaki sha mamakina wallahi kuma ki jirayi sammaci daga court na turo wasu suyiwa yar kishiyarki fyad'e...... iya bacin rai Nawaz takai domin ita gani takeyi abinda SARFRAZ yayiwa umma bai kyautaba sannan ya jaza mata Idan umminta ta dawo taji labarin abinda ya faru.... "kuka ta farayi "SARFRAZ na gode Allah ya saka da Alkhairi wulakanta umma dakayi a gabana, kuma naga ko babu komai itama ai mamana ce tunda Matar babana ce...... "heyyy shut up 😡 kafin na juyo kanki, hannunta ya kama ya jata Waje tana tutturjewa.... mota ya bud'e ya turata yasa security sannan ya zagaya ya shiga.... tukin kawai yakeyi domin ko gabanshi baya kallo, Allah ne kawai ya kaisu gida, Bud'e kopar yayi "fito " Cewa tayi "baza'a fito d'in ba" ciccibarta Yayi har saida ya kaita falour sannan ya direta gaban mummy...... zuba mishi ido mummy tayi ganin Yana cikin tsananin fushi...... kuka ya fashe dashi zaiiyi magana kuma ya kasa, sai kawai ya wuce dakinshi ya kulle... mummy ce ta Kalli nawaz "daughter meya faru da Dan uwannakine? shiru Nawaz tayi Sai kuma taga ya kamata ta fad'i abinda ya faru,,, kwashe komai tayi ta fadama mummy itama ta fashe da kuka "wallahi mummy SARFRAZ ya jazamin wahala domin idan abbana ya dawo nasan babu abinda zai hanashi tsinemin kuma nasan saiya saki mahaifiyata... Domin umma sharri zata hada Ta fad'a mishi.... cewa tayi I'm sorry "wallahi haka SARFRAZ yakeda bakar zuciya tun yana yaro Nayi Nayi na rabashi da ita Amma nakasa.... Dan Allah kiyi hakuri kuma Insha Allah abinda kike tunani bazai faruba, domin bakyada hakkin ta Hasalima ita takeda naki..... yanzu abinda nakeso shine ko zaki iya bani labarinki? nawaz tace Eh mummy zan iya baki amma akwai abinda bansaniba saidai Wanda ummina ta fada min mummy tace babu komai my daughter fad'a min Wanda kika Sani..... HAHAIFINA YA KASANCE DAN ASALIN GARIN MAIDUGURINE KUMA YAREN KANURINE *OUM AEYMAN CE 😉**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 12* *Written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji....* Supreme writers association...... Mahaifina ya kasance d'an asalin garin maidugurine ,kuma yakasance shi Yaren kanurine (babarbare) Ayanda mamana ta fadamin shine:- Tun Mahaifina Bai wuce shekara ishirinba ya auri umma, suna zaune lapia kasancewar auren soyayya sukayi, Har suka kai shekara biyar da aure amma bata ta'ba ko 'Batan wataba..... Yan uwa nata gulma Amma Mahaifina bai damuba kasancewar yanason matarshi sosai..... Ita kanta mahaifiyarshi abin ya dameta sannan kuma tana tunanin yadda zata tareshi da maganar, domin Sam dama basa shiri da umma zataga Kamar tana zuga abbana akan yayi mata kishiya.. .. Haka kaka tayi shiru batace komaiba.... Bayan shekara biyu yakasance shekara bakwai kenan da auren abbana da umma. Allah ya hadashi da ummina, takasance yar abokin baban abbana ce, domin tare ma suke gudanar da kasuwancinsu anan maidugurin...... Abu d'ayane banbancin abbana da ummina, abbana kanuri ita kuma Fulani..... Abu Kamar wasa abbana yace yanason ummina, Abu har yafito fili Kowa yasani.... Sanda umma taji labarin yi tayi Kamar zata mutu, tarika zagin kaka akan cewa ita ta Hadasu Don a wulakantata.... Ganin auren za'a yi daske yasa ta fara bin bokaye akan a Hana auren..... To abinda Allah ya riga ya tsara saida akayi bikin...... Kiyayya kuwa ummina taganta gurin umma domin kullum a zage take gurinta, gurin abbanane da kaka kawai ummina take samun sauki..... domin jininsu ya hadu Da mahaifiyar abba, saboda ko fitowa taga batayiba Saita shiga d'akin taga ko Lapia.... ummina Tasha kama umma tana zuba magani a abinci, Amma bata ta'ba damuwaba illah dai ta kiyaye yin ADDU'O'I da Bismillah. sanda ummina takai Wata bakwaine a gidan ta Fara laulayi.... murna gurin Mahaifina da kaka ba'a magana domin yi sukayi Kamar zasu cinyeta Don kulawa.... nan umma taci gaba da ba'kin ciki, ga Wata Daga zuwa zata gaje gida ita kuma shekara takwas Amma ko 'bari bata ta'ba yiba.... nan taci gaba da zuwa gurin bokaye suna cinye mata kudi, Ashe ta makara domin cikin ummi watanshi bakwai... Ashe irin cikin nanne mara laulayi kuma rabo daga zuwa Allah ya kawo... watan ummina tara agidan Allah ya Sauketa Lapia ta haifi ya Mace..... umma ji tayi Kamar ta zaune Jinjirar saboda ba'kin ciki.... ranar suna akayi shagali akasawa yarinya sunan kaka wato nawwarah, ni kenan kaka ta dauki son duniya ta doramin domin danayi ihu saitazo..... ita kuma umma tabi gari tana cewa an cuci abbana an hadashi da yar shege amatsayin yarshi, saboda anga baya haihuwa.... Domin inba da cikin tazoba yaza ayi ace Mace Wata tara ta haihu! abu har yazo kunnen abbana, aikuwa yayi burtu akan Idan ta kuma alakantamai yarinya da shegiya saiyayi mugun bata mata rai.... Domin shi yasan ayanda ya dtamu mahaifiyata da budurcinra...... nan umma tarika kuka kan cewa ummina sun asirce abba.... abun Allah, banyi shekaraba saiga umma da ciki.... nan ta Fara salo iri iri tanata kwalmade kwalmade wai ita Mai ciki.... yauda gobe har Allah yasa ta sauka lapia danta na miji... baifi Wata biyuba ya mutu, nan umma tarika ihu tana cewa umminace ta kashe mata d'a..... Ta dauki karan tsana Ta doramin, duka da hantara tun Ina karama na gane bata kaunata.... Saida Nakai shekara biyar Allah yasa umma ta haifi fauziyya... ita kuma ummina tayita faman yin 'bari, yau Lapia gobe ciwo... Bayan shekara biyu umma ta kuma haifar jamila..... Ina shekara takwas lokacin.... to tundaga nan umma itama bata kuma haihuwaba.... har Allah yasa kasuwanci ya dawo da abbana nan garin shine ya kwasomu duka... tsanar da umma take nunamin bawai ta ragu bane Sai abinda ya karu, saboda har asiri Wanda ABBA zai tsaneni takeyi...... asirin yayi tasiri ajikin ABBA Amma daidai ba Kamar yanda tasoba, saboda tasone ya saki ummi ya Kore mu, Amma sai dai kawai yayi burus damu Sam be damu damu ba kamar ba zamanshi mukeyiba.... Haka rayuwa taci gaba Muna zuwa makaranta, nayi ssce lokacin ita fauziyya tana jss1 Nayi NCE da B. Ed A federal college of education.... mummyn safraz ce tace "yanzu kenan kina nufin kinyi B. Ed? Murmushi nawaz tayi, eh mum ai shekarata 25yrs pah Mummy tace "mene? Ahaka kike shekara ishirin da biyar, kina nufin kin girma safraz kenan? shiru nawaz tahi tana murmushi "mum tace ina jinki nawaz.... fauziyya tayi aure anan kusa da gidan mu ita kuma jamila tana girls boarding school...... yanzu ni kadaice a gida sai ummina, gashi tunda abbana ya tafi maiduguri yaki dawowa Kusan shekara kenan... Gashi umma ta rufe store, bamu isa mu dauki wani abu acikiba...... dalilin dayasa na fara koyarwa a makarantar su SAFRAZ kenan.... amma daa ina gida nida ummina domin ina dinki, to kudin dinkin naga bazaiyi sustaining dinmuba shine nayi applying da naga suna neman teachers..... shiru mummy tayi "nawaz haka kikeda ilimi dama, kuma ko kadan jikinki Bai nuna shekarunkiba domin wallahi ni nazata baki wuce irin 17yrs ba..... murmushi nawaz tayi "hmm mummy haka wasu suke cemin amma sainaga Kamar sunayimin ne..... Allah nawaz da gaske nake "jikinki Nada kyau sosai.... yanzu abinda zance shine kiyi hakuri, insha Allah komai zai wuce kamar ba'ayiba domin umma zata girbi duka abinda ta shuka saboda ni natabbata Allah bazai barta hakaba....... Shiko SAFRAZ Dayake tsaye a corridor d'in dakinshi ji yayi wani tausayin nawaz ya kamashi sosai, "dama wahalar da sukesha kenan shine naso na koreta, Ashe dana koreta dana samu zunubi kuma na dauki alhakin bayin Allah.... abu d'ayane ya tayar mishi da hankali, Jin shekarun nawaz dayayi "yasan dakyar ta yarda Ta aureshi gashi kuma son nawaz slowly filled history heart ♥ unknown to him....... Ya zaiyi yanzu? Tashi d'aya ya shiga solution (wayaga saleehat n yakub an bamu assignment a anatomy ko biochemistry 😜) CHAN GIDANSU NAWAZ......... d'aki umma ta koma fuskarta tayi rudu rudu domin iya maruwa ta maru.... wayarta ta dauka ta Kira fauziyya, saida tayi missed call uku ana hudune fauziyya Ta dauka "hello umma! Dan ub*nki ina kika shiga inata kiranki baki daukaba? Ke bama wannanba Maza kizo gida akwai Matsala....... Tuni fauziyya Ta dauki gyale ko tunanin hakkin miji batayi, tayi gidansu.... azaune ta tarar da umma fuska duk ta tashi..... Umma meya samu fuskarki haka? kwashe komai umma tayi ta fadawa fauziyya, kukane ya kwacewa umma "wallahi Nawaz saitayi nadamar abinda tayi miki cewar fauziyya tana rungume umma Shawara suka fara akan yanda zasu biyowa al'amarin, magana d'aya suka yanke cewa zasu koma gurin boka suyi mishi bayanin abinda ya faru idan akwai taimakon da zai iya yi musu...... NAWAZ........... Kwance take a two sitters couch rike da wayar SAFRAZ tana d'an danne danne, amma a zuciyarta tana nazarin meyasa sarfraz zai fashe da kuka Daga fara magana..... sannan tana mamakin duk wannan girman nashi ace Ta girmeshi, itafa randa ya faɗa mata tasha wasa yakeyi... Tashi tayi ta cire hijab tana kallon dinkin shaddar jikinta "dinkin yayi mata kyau sosai Senegal design ne kuma ga kayan dass da ita. .... dai dai nan SARFRAZ ya fito daga d'aki, ya cire rigar shaddar yasa Nomal T-shirt Amma wandon shaddar ne ajikinshi ...... murmushi yayi mata ya wuce kitchen...... daskarewa tayi tana kallon shaddar jikin SARFRAZ "wai dama kaya iri d'aya mukasa? To shida yatafi yana kuka meye kuma yanzu zai fito yana mini murmushi.... fitowa yayi rikeda fruit bowl ya cikoshi da apple da pear sai pomegranate Wanda yana hannunshi ya Fara sha....... gaban nawaZ ya ajiye "bismillah malama muci" Cewa tayi "to Amma saika fadamin abinda yasa dazu ka hau yin kuka.... murmushi yayi "shikadai kikeson Sani? D'aga mishi Kai tayi "eh" Apple ya dauka ya gutsura "gaskiya nidai tun ina yaro Idan bakin ciki yamini yawa kawai Sai inji na fashe da kuka, kuma hakan yana faruwane dakanshi Bawai ni nakeyiba..... d'ago da kanshi yayi, sai ganin Nawaz yayi Tana murkususu,,, kuka ta Fara "wayyo ummina zan mutu, wayyo cikina, innalillahi wa'inna ilaihiraji'un marata zata fashe..... Rudewa Sarfraz Yayi ya Fara kiran sunan mummy...... *Oum aeyman ce 🤗* Ina Fatan Kowa yana lapia ✌🏼*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 13* Written by oum aeyman 😉 Supreme writers association........ This page is gratefully dedicated to all members of OUM AEYMAN NOVELS GROUP..... Harda Marasa comment 👀 Rudewa safraz yayi ya Fara kiran sunan mummy.... Daga stairs mum take saukowa cikin sauri "Menene Kake kwalamin Kira Haka kamar kiran mafarauta, Bata gama maganarba tayi kan nawaz da gudu ganin zata fad'o Daga kujerar.... "meya faru da ita? Ko wani abun kayi mata? A'a mummy Allah banyi mata komaiba, Muna magana kawai naji tana cewa "wayyo ummina zan mutu" Mum ta kasa daukanta saboda rud'ewa, cewa tayi "SARFRAZ ɗauketa mutafi asibiti" Ciccibarta Yayi zuwa mota, bai jira mum ba kawai Yayi igniting motar yayi Waje..... Mum data fito fad'i take "SARFRAZ tsaya mu tafi tare mana! Inah ai tuni SARFRAZ ya wuce domin yasha kwana ma..... Cewa tayi driver ya bi SARFRAZ, Amma abin mamaki ko tayan motanshi basu ganiba... Elite hospital tace suje Kila chan yaje amma ,dasuka je babu SARFRAZ babu alamunshi.... Gida tace su koma domin tasan wahala kawai zatasha saboda be dauki wayaba.... Shi kuwa goga SARFRAZ yana aeydan health care center.... Ganin yanda ya shiga da ita a hannu yasa ba'a jira komai ba aka amshesu, gado aka d'orata "Sai zufa takeyi, tana murkususu domin da alamu batasan inda takebama.... doctor ne yace please kad'an jiramu a Waje mister ..... Kopar ward d'in ya fita ya tsaya.. Sai sannan ya Kalli kanshi, babu takalmima a kafarshi babu hula rigama T-shirt ce sai wandon shadda .... Kunyar kanshi yayi ya Fara ji..... Wani ya gani yazo gurinshi rikeda takalmi, mi'ka mishi yayi "aboki sa wannan, naga sanda ka shigo a dimauce, saida na tuna sanda madam d'ina zata haihu nima, domin ni singlet cema a jikina... Amma dai yanzu ta Fara nakudar koh? takalmin SARFRAZ ya Amsa yace "nagode aboki, sannan yayi murmushi yace "aiba haihuwa zatayiba, domin ko ciki batada shi, zaune muke Muna hira sai ta Fara juye juye wai cikinta... Kyalkyale wa Mutumin Yayi da Daria "amma dai a gidanku babu mata ne koh? shanmur SAFRAZ yayi "kai kuma meye na Daria? mutumminne yace "ainaga yanda ka rudene saikace wadda zata haihu, ashema ba'kon watan tane.... dai dai nan doctor ya fito "mister pls muje office, binshi SARFRAZ yayi cikin office din, guri ya samu ya zauna. gyaran murya doctor Yayi "ehmmn dama matanka period takeyi, kuma wannan abinda kaga tanayi cramping ne saboda yanayin contracting d'in Kowa daban , wasu basuda hard contractions wasu light ne shiyasa zakaga ko suna period Amma babu Wanda zai sani... to ita irin nata mai wahalane domin irin nata mutum saiyayi aure yayi mu'amular aure da mijinshi yake denawa.... to kuma tunda ita tayi aure bata denaba sai dai asa rai idan ta haihu zata dena insha Allah.... SARFRAZ ne yace "doctor Dan Allah yanzu babu Wata hanya da za'a bi domin ta dena ko kuma wani magani da za'a bata? Doctor yace "to be sincere babu abinda za'a iya yi mata gaskiya saboda halittatta ce haka, Abu d'aya zan iya ce maka shine... duk sanda irin haka ta faru ka samu ruwan zapi da towel ka gasa mata mara Ahankali, sannan kuma tasha pain killers, Sannan yanzu zan rubuta maka wasu magunguna Sai a siya Ta ri'ka sha, Insha Allah zata samu sauki..... rubutu yayi a wata takarda ya mikawa SARFRAZ "gashi kaje pharmacy kasiyo saikazo ka dauketa. Amsa yayi "to nagode, sannan ya fita. abokinshi Wanda ya bashi takalmi ya tarar a Waje.... kafito kenan! To ya me jikin? Dasauki cewar SARFRAZ yana Kallonshi ''wai Aina kasanni? murmushi Mutumin Yayi wallahi bansan kaba kawaidai yanda naga ka dauko tane ka bani tausayi domin abin yamini kama da lokacin da matana take labour ne.. fita sukayi zuwa pharmacy, magungunan ya siya sannan suka dawo, D'akin da nawaz take ciki ya shiga, ganinta Yayi tayi shiru tana kallon ceiling. jin sallamarshi yasa Tayi sauri ta rufe ido domin kunyarshi takeji matuka... Gefen gadon ya karasa ya zuba mata ido, cewa Yayi "Allah sarki malama Ashe wahalar da takesha kenan, aikuwa zan fad'a wa umminta idan ta dawo cewa aure takeso, tunda ga abinda likita yace... Dasauri nawaz ta bud'e ido "injiwa yace maka aure nakeso 😳❓ Daria safraz yayi "ainaga sanda kika rufe ido shiyasa nasa kika bud'e da gangan.... Sham mur Nawaz tayi, irin I'm the boss d'in nan "wai Kai bazaka ri'ka bani respect na matsayina na malamarkaba..... Daria SARFRAZ Yayi "sorry my little sister 😉 Kallonta yayi ya d'an zuba mata ido, tsarguwa tayi ta Kalli jikinta don ganin me yake kallo _*MATAR RASHEED *_✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode14* *✍🏻Written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji* _*WANNAN PAGE DIN NA DUKA MEMBERS ƊIN (AK SARAKI PALACE) NE, KUMA INAWA KOWA FATAN ALKHAIRI*_ Supreme writers association....... We write with the ink of era...... That's era is our ink........ Rigar jikinta taga ta kamata sosai kuma wuyan me irin show me dinnan ne kirjinta duk a waje 'bata rai tayi "ni kadena kallona haka! Kuma Ina hijab d'ina? "malama please kiyi hakuri wallahi rud'ewa nayi, ban dauko hijab ba.... 'bata rai tayi "kana nufin Haka ka daukoni tundaga gida? "Eh Amma ai a motane kuma babu Wanda ya ganki...... "to yanzu saika nemomin Wanda Zansa Idan zamu koma gida domin wallahi bazan fita hakaba.... Fita SARFRAZ Yayi, gurin abokinshi uban surutu ya karasa "aboki Dan Allah Ina zan samu hijab? Dafa kanshi yayi alamun tunani sannan yace "muje can tsallaken akwai wata mata rana siyarda dinkakku.... Binshi SARFRAZ Yayi Kamar jela..... Gani yayi sunata yafiya kuma basu Isa gurinba, cewa Yayi "aboki wai inane gidan? Cewa Yayi "saimun shanye titinnan tukun. SARFRAZ ne Ke zancen zuci "haka gurinnan yakeda Nisa Amma mutuminnan yacemin 'can tsallaken? Baya ya juya beko Kalli mutuminba, mota ya dauko,... Saida yazo dai dai shi sannan yace shiga muje! Saida sukayi tafiyar Kusan minti goma sannan yace nanne gidan...... Parking SARFRAZ Yayi, sannan ya duba aljihunshi saura #2000 mikawa Mutumin Yayi "gashi ka amso mana don Allah... Amsa yayi ya shiga gidan, mintuna Hudu saigashi ya fito rikeda bakar Leda.... motar ya bud'e ya shiga "gashi na amso mata, Amsa SARFRAZ Yayi ya duba.... babu laipi yanada d'an girma.... motar ya tuka suka koma asibitin.... Mutumin yace to aboki nagode ku gaida gida zan shiga aikina yanzu... Murmushi SARFRAZ Yayi "ainine da godia domin ni ka taimakawa, and kuma dama anan Kake aiki? Anan nakeyin attender, kuma time d'in shigata yayi shiyasa... shiru SARFRAZ Yayi Allah sarki Mutumin babu ruwanshi, sannan yace "to aboki takalmin ka pah? kada ka damu ka tafi dashi, nizan shiga yanzu.... SARFRAZ yace "to nagode kuma Insha Allah zanzo gurinka watarana, amma ya sunanka? sunana fawaz! Allah sarki to nagode, tafiya Mutumin Yayi sannan shima SARFRAZ ya nufi d'akin da nawaz take aciki..... a takure ya ganta, mi'ka mata ledar yayi "gashi kisa mu tafi domin likita ya sallamesu tun tuni.... hijab d'in ta saka sannan ta Mike nanma kafarta babu takalmi, Cewa tayi "kana nufin Haka zan fita babu takalmi 🤨? Cewa Yayi "Ayyah sorry, jikinshi na rawa ya cire na kafarshi "gashi to kisa wannan..... kallon takalmin tayi sannan tasa, "muje to, Don kasan dai bansan hanyaba.... Cewa Yayi ''to, sannan ya fita babu takalmin a kafarshi, Amma ko a jikinshi.... seat d'in gaba ya bud'e mata, saida ta shiga sannan ya zagaya ya shiga drivers seat.... Kallonta yayi yaga tana murmushi, Basarwa yayi sannan Yayi igniting motar ya dauki hanyar gida...... shidai bece mata komai ba duk da kasan cewar yanaso yayi mata magana.... saida sukazo wucewa Ta gurin Mai suya awara,... Kalonshi tayi ''yaya SARFRAZ zanyi awara..... jiyayi zuciyar shi ta bada dammmm domin yasan babu ko 'kwandala a aljihunshi..... "zuciyarshice tace itada batada lafiya ko ya akayi har ta hango mai awara Oho.... dakewa Yayi "to bari nayi parking na siyo miki.... guri ya samu Yayi parking sannan ya bud'e ya fita, Karasawa kusa da mai awaran yayi "Assalamu alaykum, malam dan Allah akwai soyayyiya? "Eh akwai, tanawa za'a sa maka? Cewa Yayi samin ta dubu d'aya...... Zubawa Mutumin Yayi yasa yajin a gefe Dayake awaran irin wadda ake soyawa da kwai ce.... Yana mikawa SARFRAZ suka had'a ido, fasa bashi Yayi had'i da cewa "d'an gidan Alhaji!! Bud'e awarar yayi ya Kara wata yasa Aleda sannan ya mikawa SAFRAZ... gashi Alhaji 'karami kuma Don Allah ka bar kudin,,, sannan kacewa Alhaji ina gaisheshi don Allah.... Wani sanyi SARFRAZ Yaji a ranshi domin yasan bashida ko kobo.... Cewa Yayi to nagode sosai nima, kuma Insha Allah zan fad'a mishi..... cikin motar ya koma ya mi'ka mata katuwar ledar, "gashi " Cewa tayi "kanada hankali kuwa SARFRAZ? Nace zanci awara shine zakaje ka kwaso min duka awarar gurin? nifa ko ta naira dari tayimin yawa wallahi! murmushi yayi "to gatanan dai saikiyi taci ni bansan me zanyi da itaba domin banma iya ciba..... kumbura fuska tayi, tana kallon shi...... cewa Yayi "Lapia? Shikuma kallon na meye? Ko kina cikine? kallonshi tayi "me Kace? Kana nufin Kai zanso? gira ya d'aga mata "kwarai kuwa, domin kinga yaro kyakyawa son Kowa kin Wanda ya rasa..... Tun Randa na fara ganinki nasan kin kwaremin..... kai wai SARFRAZ kanada hankali kuwa? Kanne mata ido yayi "hankali original ma domin ni namijine Ke kuwa Mace, Cewa Yayi hardai bakya sona to ki Kalli cikin idona na minti biyar kacal zan yarda Allah..... Ancemaka bazan iya bane ko kuma kana tunanin inajin tsoron Kane...... d'aga idon tayi ta Kalli cikin nashi idon..... Shima cikin nata idon yake kallo.... take ya Fara tura mata sa'kon kauna da tsantsar soyayyar ta dake Dawainiya dashi.... Ji tayi bazata juri Kallonshi ba domin har idonta ya cika da kwalla, sauke kanta 'kasa tayi..... Murmushi yayi domin burinshi ya cika kuma ya samu abin tsokanarta ..... "meya faru kika sauke idonki, ko minti biyufa bamuyiba...... Dama nasan kina ciki, kuma gashi na karanci hakan a cikin idonki..... kanta na kasa tace "babu waninan nikawai bazan iya ci gaba da kallon wannan fitsararren idon naka bane domin cike yake fal da rashin kunya...... gira ya daga "haba? Aini bansan idona baida kunyaba saida kika fad'a..... kumani babu abinda na gani a cikin idonki sai tsantsar so da kauna.... "nifa malam nagaji da shirmen nan naka na yarinta, kawai ni ka kaini gida...... lebenshi ya ciza, inba tsoroba ki kalleni ki maimaita abinda kika fad'a? Baza'a kalle ka dinba....... Daria ya kyalkyale da ita "Allah sarki masoyiyata, ai tun danayi miki tambayar nan a aji kuma naga kinbani Amsa dai dai kuma babu jin kunya ko haushi nasan cewa kin kamu 😉 nifa koda kikaga Ina binki gida, ina zuwane kiganni saboda kada ki kasa barci domin dana Kalli idonki nakeganin tsantsar kaunar da kikemin..... Muryarta Kamar zatayi kuka tace, wallahi karyane ni babu wani sonka danake..... Hmmm to idan bakya sona meyasa dana baki wayata ranar farko kika Amsa... kuma nace in zama yayanki kika yarda kuma nabaki parcel kika Amsa? Sannan kuma duk rashin kunyar dana keyimiki a aji bakya damuwa... ki Godewa Allah dayasama Nasani da wuri kafin inyi budurwa, kinga kawai saimu rufawa juna asiri sabodama likita yace irin ciwonmu d'aya 'strong sexual desire' Kinga in kashe kanmu ma zamuyi a d'aki babu Wanda Zaiji..... kuka ta fashe dashi "😭😭😭😭😭😭😭 wallahi ka budemin kofar nan na tafi gidanmu... dama tunba yauba naga take takenka iri d'aya dana y'an duniya, wallahi ka budemin koparnan kafin inyi maka ihu...... wani shu'umin murmushi yayi mata "Ayyah aikin makara domin Daganan hotel zamu wuce....... Batasan sanda tace "aini period nakeyi kumani ba yar iska bace..... murmushi yayi mata "ainafiki Sani, kuma dama irinmu a haka suke kwanciya da Mace tana period domin tafi sugar......... wayyo Nashiga uku, Dan Allah ka kyaleni wallahi Niba yar iska bace Allah..... kuka ne yake so ya kwace mata, matsawa kusa da ita yayi Kamar zai rungumeta.... Dasauri taja baya , wayyo Don girman Allah ka rabu Dani...... shikuwa SAFRAZ dariyar da yake boyewace take neman fitowa... Dasauri ya hadiyeta, "to shikenan naji yanzu abinda za'a yi muje zan koya miki komai😉 kukan datake riƙe wa ne ya kwace mata "Dan Allah kada kamin komai na rokeka....... hannnunta ya kamata yana matsawa kad'an kad'an, aikingane koh? sakin hannun yayi Yayi igniting d'in motar yahau titi...... to friends Ina Fatan zakuzo ku taimaki nawaz *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 15* ✍🏻by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji (Oum aeyman) Supreme writers association (SWA).... we write with the ink of era....... That's era is our ink.... We satisfy entertain and touches our readers mind........ Sakin hannun yayi, yayi igniting d'in motar yahau titi....... Tafe suke tana rokonshi "nidai Don Allah safraz ka kyaleni wallahi ni ba irin wad'anda kake tunani bace..... Murmushi yayi "kingane koh! Zama irin hakan ba wahala bane domin Suma Wanine ya maidasu haka, kinga kenan Kema zaki iya zama koh? "Amma SAFRAZ ban ta'ba tunanin zakamin hakaba wallahi, domin ni na daukeka tamkar yayan nawa dakace.... Kuma ni duk atunanina kai kamiline...... Kashe mata ido yayi had'e da d'aga mata gira.... "kada ki damu ai hakan nake, kinji? Amma kinasona? "taɓ ai wallahi gara na mutu dana so fasikin mutum.... "haba sister maiyasa har zakiyi judging d'ina tun banyi miki komaiba... 🤨 Ai nasan zakayine shiyasa..... But nasan Allah zai kareni kuma wallahi babu abinda zaka iya yimin..... Jitayi yayi parking, kallon glass tayi tagansu a gidansu SARFRAZ. Fita yayi yazagaya, bud'e mata mota yayi "madam Mun iso! Harara ta balla mishi "wallahi baka isaba, domin ni gidanmu zaka maidani, saboda bazan kuma kwana a gidanku ba, fitsararka ta isheni wallahi ...... gabanta ya tsuguna "please malama kiyi hakuri, wallahi karya nakeyi Kuma wallahi wasa nake miki, domin abinda kikayimin a asibitine da kuma gurin mai awara shine nace saina rama .... Kallonshi tayi "hmm wai yanzu so kake na yarda dakai? "wallahi malama kawai yimiki nakeyi saboda naga kin tsorata sosai ne..... cikin idonshi ta kalla a ɗarare, ganin nadama tayi tsantsa..... zancen zuci take "to shi inba dama bashida kunyaba ya za'a yi ya ri'ka yimin wadannan maganganun kuma hankali kwance...... muryar SARFRAZ taji Yana cewa "malama kin yarda da abinda nace? Rufe idonta tayi "wallahi ni kawai ka maida ni gidanmu, babu abinda zan kumayi a gidanku tunda Kai Bakada kunya...... kafin ta rufe baki taji ya dauketa chak yayi hanyar falour da ita..... wuntsil wuntsil ta farayi "wallahi kasakeni, kasan dai haramne ta'ba macen da ba Matar kaba,, Amma kullum burinka ka daukeni, Ka maidani Kamar wana yar tsana........ banza yayi da ita.. dai dai nan ya Isa parlour, Mummy dake tsaye ta tawo da sauri "SAFuRAZ wane asibiti kaje ban gankaba? Maza kwantar da ita a sofa dinnan..... Meyasameta? Me likita yace? Ya fad'a maka matsalar? sarfraz da dariya ta kusa kamashi cewa Yayi "mum to yanzu wace tambayar zan Amsa? Kwantar da ita Yayi Gefen mum, harda Gyara mata kwanciya Kamar dama chan barci takeyi..... mummy da take a rud'e cewa tayi "halan allurar barci akayi mata? yanzu nidai SAFRAZ don Allah ka fad'a min Meyasameta? "ehmmn mummy munje aeydan hospital ne, sannan kuma likita yace wai ciwon marane, sannan wai period takeyi kuma yace wai tanada strong...... Dasauri nawaz ta Mike "wallahi mummy karyane ba Haka likita yaceba! Domin a zatonta zaice tanada strong sexual desire ne.... Batasan zaice strong contraction bane...... Dariya safraz ya kyalkyale da ita "wallahi mummy gaskiya nake fad'a domin kinsan Bana miki karya.... kuma dai likitan cewa Yayi ciwonmu iri d'ayane domin itama strong s......... tsalle nawaz tayi ta zauna a cinyarshi gamida toshe mishi baki🤫.... haba yayana! Don Allah kar kayimin haka mana...... Mummy dake zaune tana kallon drama, mamakine ya cikata domin ta rasa meye nawyaz bataso a fad'a mata. SARFRAZ kuma zaman datayi a jikinshi ji yayi barci na neman daukeshi, ga wani yanayi dayakeji a tare dashi Wanda bai ta'ba jin irinshiba. kallon fuskarta kawai yake domin koda bud'e bakin yayi bazai iyayin ko wace irin maganaba... Nawaz da hankalinta a tashe yake, ita bata sanma a jikinshi takeba Sam, domin tana Duba yanda mummy zata kalleta muddin SAFyRAZ yace tanada strong sexual desire..... kuma cewa tayi "DON Allah yayana kaji? Please kada ka fad'a wa mum, kuma wallahi hardai baka fad'a ba nayi maka alkawarin bazan koma gidan muba har sai ummina ta dawo.... karkatar da kanta gefe Tayi alamun shagwaba "kaji yayana? duk wannan abinda nawaz takeyi batasan dad'a rikita oga sarfraz takeyiba, domin shi ayanda yakeji da kuma shagwabar data keyimai ya gwammaci su dauwama a haka..... ita kuma mum dake Gefen an maida ita gunki, kallonsu take tana mamakin yaushene har suka saba haka..... addu'a tayi a zuciyarta "ayanda naga sarfraz ya natsu da nawyaz da kuma yanda yake samun nishadi IDAN yana tare da ita, sannan da irin hankalin yarinyar , ya Allah na rokeka kasa soyayya a zukatan su wadda zata kaisu GA aure, domin naga sun dace da juna..... Ganin yanda SAFyRAZ yake lumshe ido Kamar maijin barci da kuma yanda jikinshi ya saki yasa naywaz ta Kalli kanta, da sauri ta sauka daga jikinshi tana Gyara hijab, gaba d'aya kunya Ta kamata..... kasa tsayawa tayi domin jitake dama kasa ta tsage ta fad'a ciki.... da gudu tayi Hanyar kitchen ta shiga... dariya mum tayi domin tagane abinda Nawaz take nufi, Ashe bada gangan tahau jikinshiba! To nikuwa meye bataso a fad'a min dahar yasa ta fita daga hayyacinta lokaci guda? Kallon SARFRAZ Wanda yake kokarin dawowa hayyacinshi yake tayi had'e da cewa "kai SAFRAZy wai Menene Nawaz bataso KA fad'a min ne? Ajiyar zuciya yayi yace "mum damafa likitanne yace tanada strong contraction kuma asamu ruwan zafi a gasa mata maran insha Allah zai dena..... nawaz dake la'be a bakin kopar kitchen ajiyar zuciya ta sauke jin bai fad'i abinda take zatoba...... ita kuma mum murmushi tayi "hmm gaskiya nawaz akwai kunya ace Dan wannan abinne bataso a fad'a min shine harta rude Haka, harma tana aikata abinda bata saniba... SARFRAZ ne yace "mummy meye ta aikata Wanda batasan tayiba? Harararshi mum tayi "banason iskanci kana nufin da hankalinta zata hau jikinka har ta rufe maka baki, kuma hakan ma a gabana? "Au mum ai bansan wannan kike nufi ba....... Yanzu ina take? Mikewa mum tayi tabi hanyar bedroom dinta "kaje kitchen tana chan, domin sanda senses dinta suka dawo taga abinda tayi shine kunya ta rufeta har ta rasa yanda zatayi shine Ta gudu kitchen..... kai kuma dama fitsararre ne shiyasa baka damuba..... Sosa kanshi yayi "Allah ba Haka bane mum... sannan yayi hanyar kitchen d'in da sauri .... tarar da ita yayi a tsaye ta dafa kitchen cabinet, kanta a kasa tana kallon tiles.. "malama nacika miki alkawari koh? Yanzu kenan bazaki tafi ba koh? balla mishi Harara tayi "Kai wallahi kanada Matsala, da tun farkon dana cemaka kada ka fad'a da baka fad'a ba da yanzu ban aikata wannan abin kunyar ba...... yi yayi Kamar be gane abinda take nufiba "Menene kuma abin kunya? "jikinka pah nahau a gaban mum, fisbilillahi hakan ya dace? Kema dai ai tsorone yasaki domin ita kanta mum tasan bazakiyi hakan da niyyaba..... Amma dukda Haka kiyi hakuri kinji? bata rai rai tayi "A'a nidai, sai dai idan zaka aramin wayarka na Kira ummina! SARFRAZ daya zuba mata ido "aranshi yace da tasan abinda nakeji IDAN tana wannan shagwabar wallahi da bata rinka yiba..... cewa Yayi bari naje na dauko miki, tana dakina....... murmushi tayi "to Amma kayi sauri kaji? d'aga mata Kai Yayi, ya fita da sauri...... Baifi minti biyar da fitaba ya dawo rikeda waya, mi'ka mata Yayi "gashi ki kirata koh! Amsa tayi tasa number ummi a ciki sannan tayi dialing, Kara biyu ana uku Ta d'aga "Assalamu alaykum, Wa'alaykis salaam "ummi na" Ummi tacan bangaren tace nawaz! Inata kiran wayarki sai dai inji namiji ya Amsa, walahi har hankalina ya tashi.... "Wallahi wayarce ta nace ummi , cewar Nawaz cikin zumuɗi "To Masha Allah tunda kina lafiya, ummi tace ta daya bangaren "ummi na kin sauka Lapia, yasu dada da baffa? "Sunanan Lapia, kuma dama ina ta kirankine domin baffa yace bai yarda in barki Ke kadai ba, wai Lallai Lallai ki taho gobe.... tsalle nawaz tayi "ummi Dagaske? Aiko insha Allah gobe da Sassafen zan shirya...... SARFRAZ dake gefe jin tana cewa gobe da safe zata shirya yasa ya kwace wayar ya kashe sannan ya kalleta "ina zakije dazaki shirya da Sassafe?? _*MATAR RASHEED*_❤️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 16* ✍🏻written by oum aeyman Supreme writers association, 🙏🙏🙏🙏Ina Fatan duka members suna Lapia.... "ina zakije da zaki shirya da sassafe? A yatsine ta kalleshi, "wai Kai SARFRAZ me kamaidani ne? Da yardar ka nakeyin wayar nan amma yanzu ban gamaba ka wani amshe, Ai koma dai Menene yakamata kabarni na gama wayar ko? Kuma sanin kankane da ummi na nake waya. "naji kuma na amshi laifin ban kyautaba, Amma jin kince zaki shirya da sassafe shine naji bazan iya jurewaba wallahi. And please don Allah ki fad'a min Ina zakije? Dad'a murtuke fuska tayi "ummi ce tace na shirya naje maiduguri na sameta wai kakan Nina sunata yi mata fad'a, saboda tabarni a gida ni kadai. SARFRAZ ne yaji jiri na neman kwasheshi, ''and Nawaz yanzu dan Allah sai Ki tafi ki barni? dariya Nawaz tayi "dagudu ma? Dama wallahi nagaji da yarintarka da rashin kunyar ka... Hmm inma kana ganin karyane Allah ya kaimu gobe kagani. Jiyayi duniyar tamishi zafi, dukda sanyin da akeyi ji yayi zufa na neman feso mai. Mamaki yahau yi azuciyarshi "nashiga uku, yaushe ne zuciya ta saba da ganin Nawaz dahar nakejin Kamar zan mutu Don zata koma gun mahaifiyarta? yanayin yanda SARFRAZ Yayi laushi yasa NAWAZ taji ya d'an bata tausayi, "SAF meya faru naga kayi wani iri? tsugunawa yayi "Dan Allah Dan khaunar annanbi, please malama ki taimaka min Karki tafi, wallahi idan kika tafi komai zai iya faruwa.. dariya ce taso kwacewa NAWAZ, sauri tayi ta shanye kada ya gane. "to yanzu ya kakeso ayi? SARFRAZ yace "kawai ki fad'a mata cewa kin samu Wata mumyn, kuma tana kula dake, nasan idan su kaka sukaji Haka zasu hakura su barki ki zauna, Inyasoma gobe da safe Sai mumy ta kirata suyi magana... "nifa gaskiya nasan halin kakan Nina domin dakyar in zasu amince, kuma nasan dole su tambayi ya akayi na bar gida? kaga dole a fad'a musu abinda ya faru, nikuma gaskiya banason abinda zai tayarwa da mahaifiyata hankali. "Kallonta yayi, okay to bari nazo,. Tana tsaye tana jin dad'i zata gurin umminta da Dada, Mamaki takeyi "Yoshi SARFRAZ ina abinda ya shafeshi, Don zan tafi abuna meye na wani damuwa..... parlour Ta leka a hankali, ganin babu mumy yasa ta koma ta zubo awararta a plate ta dauko ruwa Sannan ta fito ta zauna a Saman sofa tanaci tana murmushi.... Shi kuwa goga SARFRAZ gurin mummy ya wuce, yana shiga d'akin ya fashe da kuka "mumy nashiga uku, wallahi ni nasan mutuwa kawai zanyi. damuwace 'karara ta nuna a fuskar mummy "sweetheart meya faru da kake cewa Kai mutuwa zakayi? Bakada lapiya ne? ko ciwon cikin Kane ya tashi? juyoshi tayi ta d'ora kanshi a Saman cinyarta, please sweetheart kayimin magana mana,. Hawaye na zuba a fuskarshi yace "mumy NAWAZ ce wai gobe zata tafi maiduguri gurin umminta, kuma kinsan idan ta tafi bazata kuma zuwa gidannan ba sai dai kawai Idan Mun hadu a makaranta. ni kuma gaskiya bazan juri hakaba, domin idan ban gantaba wallahi zan iya mutuwa, saboda "I LOVE HER WITH ALL MY HEART " Wallahi mummy Ina sonta sosai, kuma ni ita zaki fadawa dad ya auramin..... dad'i mommy taji aranta, saboda Wanda ake cewa Yayi aure yana kuka, yau shine kacewa ga wadda za'a aura mai. Sanyi tayi da muryarta, sweetie kada ka damu ai wannan mai saukine har dai zancen dad ne, yanzu Matsala d'aya nake tsoro! Da sauri SARFRAZ ya tashi zaune, mumy please macece matsalar? "matsalar itace shin NAWAZ zata soka, kuma zata yarda Ta aureka? Domin shi aure ana sone duka bangare biyun suso junansu... Kuma ma in banda rigima irin taka, Nawaz fa ta girmeka, kuma daka kalleta kasan cikakkiyar macece, ina zaka kaita..... bata rai yayi ''haba mummy keda zaki samomin mafita ai be kamata kina wannan maganarba, ni dae ina sonta a Haka, kuma ai nima Inada girma domin Nafita kiba har tsawoma kuma ko jerawa mukayi ni za'a dauka a matsayin yayanta...... nidai mummy ki nenomini mafita yanda zata soni itama.. dariya mummy tayi "ooh SARFRAZ yau nice aka maida Kamar wani aboki.. Ko irin kunyar nan ta uwa babu.... bata rai SARFRAZ Yayi domin duk ya kagu dayaji me mummy zatace a matsayin Shawara, "ni dai mummy Don girman Allah abar wannan maganar, nidai kawai ki bani shawarar..... dariya mumy tayi "kana jina, ka zama mai kyautata mata, ka rika nuna mata kulawa sosai fiyeda yadda hankalinta zai iya dauka. sannan ka ri'ka nuna mata kauna tsantsa. ka kara da nuna kishinta, sannan Abu na faruwa da ita ka nuna damuwa fiyeda yadda ita zata nuna... Kuma shine ba garangatsau zakace kana sontaba, saika had'a da system. kaga misali duk abubuwan dana lissafamaka babu macen dazaka ri'ka yiwa haka batayi burin kazama mijintaba. Ahankali itama sonka zai shiga ranta bata saniba.... kaga Bayan Kace kanasonta zai zama ka bata two options kenan, zaka sata tunani, domin zataga idan tace bata sonka tayi maka butulci na biyu kuma shine, zataga tayiwa kanta asara domin bata San waye kuma xaixo yace yana sontaba.... da sauri zata amince domin mata akwaisu da kishi, zataga bata zama matarkaba ma kana mata hidima balle tazama, kuma zatayi tunani idan ma taki amincewa wata zaka dauko kuma ka ri'ka yi mata haka... Da gudu zata yarda.... murmushi SARFRAZ Yayi "to ai mum Kusan wadannan abinda kika fad'a Ina mata su, Sai dai naga Kamar baiyi aikiba.... mum tace "SARFRAZ dad'ina dakai wutar ciki, kacika hanzari. ai zakayita yi mata hakane sai an dad'e zaka gane Yana aiki. dariya yayi ya rungume mum "whoooooah saini sweetien mamanshi nagodema Allah daya bani Ke a matsayin mahaifiya..... tashi Yayi "mum bari na koma gurinta, sai ince tashigo d'aki kafin dad ya dawo, mum tace "kada ka damu yau zanyi wa dad dinka maganarta, kaga koda ya ganta babu Matsala.... murmushi yayi "to mum nagode, bari naje..... fita daga d'akin mum yayi yanajin gaba d'aya Allah ya yaye mishi damuwarshi. a sofa ya ganta zaune ta tasa uban awara tayi Tagumi, harya karasa gurinta bata San yazoba. ta'ba hannunta Yayi, firgitgit ta dawo hayyacinta "murmushi yayi mata "ya akayine? chino baki tayi Kamar zatayi kuka "bakai bane Daga nace maka zanci awara shine zakaje ka kwaso min duka awarar nan sai Kace Wanda mutum ishirin zasuci. yanda tayi maganar ta burgeshi, "okay to yanzu ya kike ganin za'a yi? "ni naci guda Hudu kuma na koshi, yanzu kaima kaci idan ka rage kuma kasan zata lalace. "A'a sai dae muci tare domin guda Hudu tayi miki kadan, yanzu ki kara nima kuma zanyi taci har saina koshi..... murmushi tayi"dagaske kaima zakaci? "Eh zanci duk da dai ban ta'ba ciba nasan zan iyaci saboda Ke. d'aya ya dauka ya gutsiri kad'an, Ahankali yake taunawa, dakyar ya hadiye domin ji yake kamar ƙwai amma wani iri. tausayi ya bata "dena ci kada kayi amai, bari na kara guda biyu Sai asa sauran a fridge, gobe sai aba almajirai tunda kaga bananan. amma kuma gaskiya idan na kuma cewa ka siya mini abu kada ka siyo Mai yawa, domin asara batada dad'i kuma babu kyau zubar da abinci. to Insha Allah zan kiyaye, sannan kuma ko wannan awarar da kika gani ba siya nayiba kyauta Mutumin ya bani . in an amazed tace "kamarya kyauta? Tashi Yayi ya zauna a kusa da ita ya dau awara guda daya ya nufi bakinta dashi "kedai bud'e in baki idan kin koshi zan baki labarin abinda ya faru duka, Bud'e bakin tayi ta gutsuri kad'an, be dauke hannunshi ba Yana cewa "ki kara mana.. dad suka gani akansu tsaye, murmushi dad yayi "A'a sannunku da dare, SARFRAZ bakuwa mukayine? SARFRAZ Yayi murmushi "Eh dad ai tun tunima tananan, Ita kuwa Nawaz ji tayi Kamar ta zabga ihu, saboda wata irin kunya data kamata......... OUM AEYMAN CE.........*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 17* ✍🏻written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji (*Matar Rasheed*) Supreme writers association..... (SWA) we write with the ink of era... That's era is our ink... We satisfy, entertain and touches our readers mind.... Saboda wata irin kunya data kamata. D'aki dad yawuce, da sauri SARFRAZ ya Mike ya shiga d'akin mum.... "mum wallahi yanzu dad ya dawo kuma ya ganni inaba Nawaz abu a baki... "wallahi SARFRAZ gaba d'aya kazama mara kunya cewar mum tana hararar shi..... Ni wuce ka fita ka bari guri..... Sime Sime ya fita, bega Nawaz a inda ya barta ba, dube dube ya farayi Yana tunanin ina ta shiga...... Motsi ya jiyo a kitchen, nan yagane tana ciki,. Shiga kitchen d'in Yayi "malama kin koshine? Kallonshi tayi kamar wadda aka ce babanta ya mutu ba'a saniba, namma kabiyonine ka bata min sunan? Cikin damuwa SARFRAZ yace "menayi kuma malama? Ba'a saniba, kuma Insha Allah gobe karfe shidan safe nabar maka gidanku inyaso duk abinda zakayi sai kayi..... Sanda zaka bani warar Kamar kada na Amsa, Amma sai naga idan ban amsaba Nayi maka wulakanci.... kuma kaga tawowar daddy maimakon ka Dena bani amma sai ka'ki fadamin yazo... Ayyah "wallahi malama nima bansan sanda dad ya shigoba, wallahi sanda kika ganshi nima lokacin naganshi.... Na rantse da Allah kinsan nima bazan so hakaba, ai babu dad'i, Dan Allah kiyi hakuri... Kallonshi tayi, naji! zanje nayi wanka na shirya, inaso nayi barci..... To muje d'akin mum domin ta tafi d'akin daddy.... Cewar sarfraz yana murmushi... Gaba tashiga yabi bayanta, har bedroom d'in mum ya rakata.... kama kwankwaso tayi "to katafi nagode saida safe,... murmushi yayi "to Allah ya tashemu Lapia, sannan ya Mike ya fita parlour.... inda ta ajiye doguwan rigar da Mum tabata ta Duba, nan taga panties da ragowar pads dinta.. cire kayanta tayi sannan ta daura towel ta shiga bayin, tafi Kusan minti ishirin tana wanka sannan ta wanke pant dinta da skirt, tayi disposing d'in pad d'in data cire... wani towel taga anyi hanging, shi tajanyo ta tsane jikinta dashi, sannan tasa sabon pad Ta fito daga bayin.... Gefen gado ta zauna tayi shiru, na Kusan minti uku, sannan ta Mike... Gaban dressing mirror Ta karasa Don shafa lotion...... motsi taji a bayanta, koda ta waiga bataga kowaba... juyawa tayi ta dauki cocoa butter ta fara shafawa a fuska sannan hannu..... SARFRAZ dake la'be Bayan labule yabi bayanta Wanda gashi ya barbaje da kallo..... dai dai nan ta Fara shafawa a cinyarta, tadanyi sama da towel d'in duk abinda take SARFRAZ Yana Kallonta, jiyayi tsigar jikinshi ta fara tashi "meyasa nashigo d'akin nan? Ina zaune Lapia zan tayarwa da kaina hankali..... gaba d'aya ta tattare towel d'in a kwankwasonta tana shafawa a duka cinyarta.... Gaba d'aya mood d'in SARFRAZ ya chanza, haushin kanshima yakeji.... Mikewa Yayi ta nufi inda doguwar rigarta take, dai dai santar inda SARFRAZ yake a la'be..... rigan ta dauka ta juyata daidai, Hannu tasa zata zare towel d'in, da sauri safraz ya rufe idonshi domin a halin yanzu shiyasan irin abinda yakeji..... rigan tasa sannan ta koma gurin mirror d'in, taje kanta tayi sannan tayi parking dinshi in a Messy bun... turare ta fesa kad'an sannan ta dauki karamin gyalen rigar ta yane kanta dashi.... cire zanin gadon tayi ta karkabe, sannan ta mayar tayi tucking dinshi.... Hawa gadon tayi "mtsews ace mutum ya nemi wayarshi ya rasa, fisbilillahi yanzu da tananan ai da Nayi game yanda banajin barcin nan.... shiru tayi tana tunani, can kuma tace "wai Anya SARFRAZ dinnan kanshi d'aya? Nidai Kamar mai aljanu, inba mai aljanuba, kawai saika dauko Mace ka ajiye ta a gidanku kana mata hidima..... amma nasan jininmu ya hadu domin wallahi da Wanine yakemin abinda SARFRAZ yakemin da yasha wahala wallahi.... Jifa irin tambayoyin da yakemin "yaya ake wankan janaba? Yaya ake kwanciya da Mace? Wace macece tafi dad'in muamula? wallahi nidai wadannan tambayoyin na gwammaci na mutu bansan Amsar suba da in yi tambaya akansu.... Itama mamanshi ta yarda Dani daga zuwa, da ace ni mayya cefa? uhhmm koda yake gobe dai zan tafi in huta da farintar SARFRAZ.... dariya ta kyalkyale da ita "oh shima harda zuwa gidanmu, ita kuma umma harda yin ba'kin ciki batasan ma karamin yaro bane.... Duk wannan sambatun da takeyi SARFRAZ Yana jinta, Abu d'ayane ya dameshi, jinshi da yake Kamar bashiba ga wani nauyi da idonshi ya mishi yana jinshi Kamar d'an Maye, photon jikin Nawaz ne yaketa mishi yawo a zuciya.... Gashi ya gaji da tsayuwa, so yake ya samu ya kwanta inda hali ma ya kwanta kusada Nawaz.... Adduar kwanciya barci ta karanta sannan taja light duvet ta rufe jikinta ta d'ora kanta a pillow. a hankali sarfraz yake tafiya yanaso ya fita a dakin domin halin dayashiga komai na iya faruwa "he's totally in need of her" Yana bakin kopa Yana tunanin yanda zai bud'e kopar ya fita, yaji motsin Nawaz... Dube dube takeyi akan gadon domin ji tayi Kamar abu yana yi mata yawo a jiki, Bataga komaiba ta koma ta kwanta... kwantawarta keda wuya taji ana yi mata tafiya a gadon bayan ta. da sauri ta mi'ke tahau zazzage rigar tana bubbuga kafarta..... tsaka ce (gecko) 🦎ta fado daga cikin rigar, aikuwa da gudu tayi hanyar Waje Tana ihu, tana kokarin bud'e Kopa taji ta kuma ta'ba abu Kamar mutum... nan takuma dagewa zata zabga wani ihun Da sauri SARFRAZ ya fito fili had'e da toshe mata baki.. Ganin SARFRAZ ne yasa ta karasa kusa dashi ta rungumeshi tana maida numfashi. sosai ta kamkameshi jikinta sai rawa yakeyi.. cikin wata irin kasalalliyar murya yace "meya farune? muryarta na rawa tace "tsaka ce ta shigan mini cikin Rigaa. Nidai Don Allah ka fitar Dani Daga nan tsoronta nakeji sosai... Lumshe idonshi Yayi ya dad'a rungumeta, a tunaninshi zai samu sauki Amma Ina jiyake abin Yana dad'a karuwa Kamar ana zuba fetur a wuta... cikin muryarshi dashashshiya yace "sakeni kigani, A hankali ta sakeshi, aikuwa tana sakinshi yayi Waje da gudu, itama da gudu ta bishi ta rungumeshi Ta baya tana cewa "Don Allah sarfraz kada ka gudu ka barni wallahi tsoronta nakeji hadda hawaye a fuskarta.... ganin yanda hankalinta ya tashi yasa SARFRAZ yace "to shikenan kada ki damu zauna anan inje dakina in dawo... ai kuwa jin haka yasa ta dada kamkameshi nidai A'a Don Allah muje tare zan rakaka.... "Nawaz ki sakeni! Da kinsan halin danake ciki da ko kusa Dani bazaki matsoba. "Eh naji nidai ko wane hali kake ciki naji zan bika... Don Allah... bece komaiba ya Fara tafiya, binshi takeyi domin hannunta Yana sargafe a kwankwasonshi .. Suna shiga d'aki ya fad'a gado Yayi ruf da ciki yana mutsu mutsu..... hankalin Nawaz yayi mugun tashi ganin yanda sarfraz yakeyi... Kusa dashi ta karasa "meke damunka? Dan Allah ka fad'a min... Ahankali ya bud'e ido ya kalleta '' "cikina Nawaz zan mutu, don Allah ki kiramin mum" hankalin Nawaz ne ya dada tashi, gashi kuma yace zai mutu... Wayar ta dauka ta gama dubawa amma babu mum a sunayen.. cemai tayi dame kayi saving d'in number? Ahankali yace "my World " dubawa tayi tayi dialing da sauri, amma sai taji wayar a kashe.... cewa tayi wayar mum a kashe take yanzu yaza ayi? bata gama rufe bakiba ya janyota ta fada jikinshi ya rungumeta da karfi Laluben bakinta ya farayi......... ink d'ina ya kare 🖊 Kubiyoni donjin nawaz kuwa tana kubuta a hannun oga SAFRAZ??? *MATAR RASHEED CE.....*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 18* 🤳written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji Supreme Writers Association We write with the ink of era..... That's era is our ink.... We satisfy, entertain and touches readers mind..... Laluben bakinta ya farayi, Mai kuma ya tuna Oho, sai ya fasa...... Nawaz data ke kokarin kwace kanta tana rayawa aranta cewa "wai meke damunshine? Ji yanda jikinshi Yayi zafi, sannan ya wani rungumeni salon mamanshi ta shigo ta zata ni yar duniya ce.... Nasan kuma shi cewa zaiyi besan sanda ya rungumeniba.... Kusa dashi ta matsa "kanada maganine ka fad'a min inda yake in dauko maka? Can murya cikin makogwaronshi yace "kije kitchen ki dauko lemun tsami🍋 guda biyar ki yanka ki matse ruwan saiki bud'e fridge zakiga zuma, saiki zuba cokali uku.... Ki kawomin insha, Da sauri Nawaz tayi kitchen hankalinta a tashe.... Cikin y'an minute ta had'a mishi, d'akin ta koma da sauri... "gashi na had'a maka, tashi kasha kaji? Gadon ta hau Ta d'ago shi a hankali, kopin ta kafa mishi a baki, tunda ya farasha saida ya shanye duka... Pillow tasa mishi sannan ta d'ora kanshi a hankali..... Rufe idonshi Yayi yana cije lebenshi.... "Sannu kaji" cewar Nawaz wadda hankalinta yake a tashe Kai kawai ya iya d'aga mata, sannan ya Gyara Kwanciyarshi, yaja bargo ya rufe jikinshi.... Zaune take tanata Kallonshi har sama da awa d'aya, tananan zaune barci ya Fara daukarta... Jin zatayi barcin da gaske yasa ta tashi ta Duba yanayin jikin nashi, Jitayi zafin ya sauka sannan kuma yanata zufa.... Sai barcin daya keyi a hankali.... Ganin yaji sau'ki yasa ta koma Saman three sitters couch d'in dake Gefen gadon ta kwanta... Ko minti goma cikakke ba'a yiba barci Yayi awon gaba da ita.... Can cikin dare Misalin karfe uku SARFRAZ ya tashi domin wani irin fitsari dayaji ya matseshi... Nawaz yagani kwance Saman couch Amma hannun Ta ri'ke da bargon daya rufe jikinshi dashi.... Wani guntun murmushi yayi "dama duka wannan abinda takemin kaunace tasa Haka! Amma nasan tausayine kawai irinna malama Nawaz,,, Mikewa Yayi ya nufi bayi, Bayan ya fito ya zauna Gefen gado ya kura mata ido "kalleta mai kyau, kuma ga yarinta nan a fuskarta, Anya ba karyar shekaru take yiba? uhm ni wallahi ko shekararta d'ari haka nake sonta " hannu ya had'a guri guda 🤲🏼"ya ilahi kasa wannan baiwar taka ta kaunaceni koda kuwa kwatan kaunar danake matane.... yanzu kuma gobe zata tafi, wani irin shu'umin Murmushi yayi "hmm nasan abinda zanyi, Allah ya kaimu goben Lapia... ganin yanda take barcin cikin natsuwa kuma hankali kwance yasa shi tuna ta'asar dayaso Yayi..... Baki ya kama 🤔oh yanzufa da bankai zuciya nesaba da yanzu wata chapter akeyi ba barcin namba.... ya Allah nagode maka dakasa nafi karfin zuciyata 🤲🏼.... itace batasan yanda nakejiba Saita ri'ka yimin shagwaba sannan kuma Inaga Anya malama tanada cikakkiyar Lapia kuwa, domin da tanada cikakkiyar Lapia data gane moves d'ina da kuma abinda nake nufi, amma Sam ni sainaga jikintama baya responding ....... Addu'a yayi ya shafa mata sannan shima yayi ya shafawa kanshi, kwantawa yayi ya ri'ke hannunta cikin nashi, da burin Allah yakaisu safiya lapia..... 5:29am Nawaz ta tashi a firgice, da sauri ta karasa fuskar SARFRAZ, ganin Yana numfashi yasa tace "ALLAH nagode maka, naji jikin nashima Yayi sauki, Allah yasa kada ya karayin irin wannan ciwon domin ya azabtar dashi...... Gashi mummyn shima bata saniba...... Kiran sallar asbah taji, To yanzu yaza ayi in tasheshi, ban saniba ko zazzabin da saura... duk wannan abinda Nawaz takeyi SARFRAZ Yana jinta domin dama idonshi biyu ganin Ta tashine yasa ya rufe idonshi.... a hankali tadan bigi kafanshi, SARFRAZ! SARFRAZ!! Tashi asbah tayi... Juyawa yayi alamun maiyin barci sannan yace 'uhhmm? Dad'a cewa tayi "ka tashi kayi sallah an Kira kada a tayar bakayi alwala ba.... Tashi Yayi zaune Yana Mitstsike idonshi, Kallonta yayi "kada dai ace anan kika kwana? d'aga kanta tayi "Eh anan na kwana saboda jikinka, kuma sanin kanka ne bazan iya tafiya nabarka a halin da Kake cikiba...... Murmushi SARFRAZ yayi "oh Ashe dole nayi mafarki, Ashe da Mace na kwana, .... A yatsine ta kalleshi kamarya da Mace ka kwana? Kuma wane mafarki kayi? TASHI yayi yabi hanyar bayi sannan ya waigo "mafarki Nayi na kwanta dake, kuma gaskiya ya kamata ki Duba kanki kiga badai da gaske nayiba koh? Domin mafarkin yafi kowanne dad'i Dukda dai naga Ke Bakida service.... cikin bayin ya shige yana dariya.... wani makokon abune yazowa Nawaz wuya "wannan yaron bazai ta'ba iya dena rashin kunyaba, ace naji tausayinshi nazo na kula dashi shine zai kalleni yace yayi mafarki Dani, a tunaninshi ni sa'ar shice? Yanzun nan zan had'a kayana, idan na bar mishi gidan zanga wadda zai gani arha balle har ya ri'ka fad'an mata abinda yaga dama..... fita tayi daga d'akin ta nufi na mummy, tana shiga mumy tana shigowa, Murmushi mummy tayi "daughter keda bakya sallah Aida kinyi barcinki baki tashiba, barin ga tafiya mai tsawo a gabanki.... Murmushi Nawaz tayi "uhhmm mummy dama cewa nayi yanzu zanyi wanka sai in shirya, zuwa shida in tafi gida sai in had'a kayana saboda sammako nakeso nayi..... mum ce ta dafa kafadarta "calm down my dear duk wannan hanzarinfa? kin manta cewa SAUKA LAPIA AKESO BA SAUKA LAHIRABA? yanzu abinda nakeso dake shine kiyi kwanciyar ki, kuma gida da kike cewa zakije basai kinjeba domin anan zan had'a miki komai da kikeso..... pillow mummy ta janyo ta kwantar da Nawaz sannan tasa mata duvet ta rufeta..... Dayake dama ba wani barcin kirki tayiba yasa batafi minti biyarba Ahaka ta shiga duniyar barci... Misalin 7:30am SARFRAZ ya shiga d'akin dad domin gaisheshi.... murmushi dad yayi "A'a Kace fabulous d'ina ne yazo mu gaisa! Murmushi SARFRAZ Yayi "Eh dad.... Bayan sun gaisa dad yace.... ai jiya mummyn ka tayimin bayani akan Nawaz, Ashe y'ar y'ar kawartace, tacemin mahaifiyarta taje MAIDUGURINE shine ta kawota nan gidan zuwa ta dawo... kuma saigashi naga har kun saba.... Dadne ya kashewa SARFRAZ ido 😉 my son Kodai da ita zaayi..... Murmushi SARFRAZ Yayi yana Sosa kai, Dai dai nan mum tashigo rikeda waya.... Alhaji kaji wai kakannin Nawaz sun matsa wai Lallai ta tafi yau, wai sai fad'a suke yi.... 'Toh yanzu yaza ayi? Cewar dady yana kallon hajiya.... Ehm ina tunani kawai SARFRAZ ya kaita, inaga zaifi data yita jigila a hanya, koya Kace Alhaji? murmushi Alhaji yayi Eh hakan Yayi, kinga dama shima ya dad'e beje gurinsu kakaba kinga saiya biya can koh? SAF6RAZ kuwa ji yayi Kamar anyi mishi bushara da gidan Aljannah domin mummy ta shirya komai.... Mummy tace "SARFRAZ tashi muje inyi maka list kaje kasuwa ka siyowa su mama tsarabar dazaka Kai musu.... Binta Yayi abaya, suna fita ya daka tsalle ya rungumeta Ta baya" gaskiya ina kaunarki mum, Ina Fatan Allah ya biyaka da gidan Aljannah..... murmushi mum tayi "ni nayi wannanne kawai domin Kai, yanzu muje inyi maka rubutu, domin inaso kayi siyayyya da yawa, kaga zaka siyowa nawaz dogayen riguna da hijabs da waya dasu takalma harda jaka da pause koda guda biyune, kuma sannan inaso kaje gidan hajiya Bilki ka amso mata atampopi da lace dinkakku koda material ko shadda Wallahi bani da Lafiya ne kwana biyu, ina barar addu'ar ku. *MATAR RASHEED*✍️🎀🎀 *SARFRAZ*🎀🎀 *episode 19* *✍🏻written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji* *SUPREME WRITERS ASSOCIATION (SWA) .... We write with the ink of era, that's era is our ink..... We satisfy, entertain and touches our readers mind.....* Inaso kaje gidan hajiya Bilki ka amso mata atampopi da lace dinkakku koda material ko shadda, Saika wuce kasuwa ka siyowa su inna Suma atampopi dadai sauran abun Bukata, yanzu dai zauna in gama rubutamaka. Zama yayi a Gefen mum Don babu yanda ya iya, saboda shi yasone yaje d'akin mummy yaga Nawaz saboda bega giftawartaba .... A Saman table ta dauki jotter, na Nawaz ta fara rubutawa sannan ta rubuta Wanda za'a kaiwa y'an uwa..... Cewa SARFRAZ tayi biyoni d'akin daddyn ka... Kumbura baki Yayi sannan yabi bayanta, suna shiga mum tacewa daddy "kaga abubuwan dana rubuta sunyi? Amsa dad yayi ya Duba "Eh sunyi amma sainaga baki wani rubutawa ummanki abubuwa da yawa ba, gaskiya Ki kara..... Murmushi tayi "to Alhaji nagode Allah ya saka da Alkhairi! D'aga mata hannu Alhaji Yayi "dakata! Wai so nawa zance miki ki denamin godia ne? Gaskiya banso ki dena. Murmushi mummy tayi "to Allah ya huci zuciyarka, kuma naga ai duk Wanda bai iya godewa mutumba bazai iya godewa Allah ba. SARFRAZ ne yace mummy bari nazo.... Da sauri mum tace "A'a babu inda zaka, amshi takardar nan kawai ka tafi yanzu, inyaso saika fara zuwa gidan hajiya Bilki tukuna.... Amsar takardar yayi ya fita, dad ne ya kwala mishi Kira "fabulous zo mana..... Dawowa SARFRAZ Yayi Amma ranshi a had'e, "gani dad" Murmushi dad yayi "kafita banbaka master card 💳 ba, to dame zakayi siyayyar? Dad akwai kudi a account d'ina ai..... Hmm wannan ai nakane, yanzu amshi wannan saikayi siyayyar, idan kagama komai saika ajiyemin a drawer.... Amsa yayi "to dad nagode " Girgiza Kai dad yayi "kaima mummyn taka ta koya maka Dabi'ar ta ta godia koh? shi dai SARFRAZ fita yayi, parking space ya wuce ya shiga mota ya fita daga gidan, daka kalleshi zaka gane yana cikin damuwa...... Bai wuce ko inaba sai gidansu ABDUL (abokinshi na islamiyya) yana shiga kuwa yaci Sa'a, dashi ya Fara haduwa....... D'akin ABDUL suka koma, ganin ABDUL Yayi duk shashin bulala a jikinshi Dayake singlet ce a jikinshi...... Mamakine ya kama SARFRAZ 🤔😳, Kai kuwa ABDUL waye yayi maka wannan danyen aikin? murmushi ABDUL Yayi "SARFRAZ Allah yasoka kabi malama Nawaz ka tafi gida ranar nan, wallahi dabansan yanda jikinka zaiyiba barin gaka fari! Ai in takaice maka zance, katuna sanda zaku fita ai malam bilal ya shigo ajinmu koh? SARFRAZ ya daga kai alamun "eh Abdul yaci gaba da cewa" to wallahi daya fara dukanmu Kai kazata Allah ne ya aikoshi.. domin maganar danake maka yanzu haka Zainab da uthman suna asibiti harda Karin ruwa akayi musu...... tausayine ya kama SAFyRAZ ganin irin yanda y'an ajinsu suka shiga halin ha'ula'i kuma duk sabo dashi..... cewa Yayi "ABDUL amma ya fad'a muku abinda kukayi mishi..... Girgiza Kai ABDUL Yayi "A'a wallahi baice mana komaiba.... Kai in banda abinka SARFRAZ waye baisan mugunta irin ta malam bilal ba? Dafashi SARFRAZ Yayi "Dan Allah kayi hakuri, wallahi be kyautaba, ai duka ba hauka bane...... Hmm SARFRAZ Idan banyi hakuriba to me zanyi? Cewar ABDUL yana Mikewa "bari na kawo maka flask ka hada tea domin nasan baka karyaba.... Cewa Yayi to abokina... ABDUL na fita SARFRAZ yace "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un, yanzu abinda malam bilal yayi musu kenan, wallahi danasan abinda zaiyi kenan daban Kira shiba.... Fisbilillahi ji yanda ya illata musu jiki! Dai dai nan ABDUL ya shigo rikeda vacuum da warmer ya ajiye a gaban SARFRAZ "gashi bari na kawo maka mug da plate. komawa Yayi, baifi three minutes ba ya dawo da plate da mug..... hadawa SARFRAZ tea Yayi sannan ya zuba mishi doya da kwai Wanda yaji kayan miya Sai kamshi yakeyi.... a ka'idar SARFRAZ bayacin Abu mai nauyi da safe, iya kacin shi yasha tea da bread shima bai wuce yanka biyuba, ko kuma ya hada da kwai. Amma jin kamshin doyar yasa yaji sha'awar yaci, sosai yaci doyan, bayin ya shiga ya dauraye bakinshi ya wanke hannu..... zama yayi a Saman gado suka fara hira shida ABDUL, gyangyadi yaji Yana kamashi.... Abdul banacin abinci me nauyi da safe, gashi naci doyar nan tasamin nauyin jiki, yanzu haka barci nakeji.... dariya ABDUL Yayi "to kawai ka d'an kwanta kad'an Kona minti talatin ne koh, cewa Yayi to, 'Dan bani duvet, kasan Bana iya barci Idan ban rufe jikinaba.... nan SARFRAZ ya kwanta ya Fara barcinshi hani'an sam yama manta da Aiken mummy... *THREE HOURS LATER* *that's 10:45am* SARFRAZ nagani kwance yanata faman barci Kamar Wanda yake a gida..... Shi kuwa ABDUL mamanshi ta aikeshi ya tafi.... *gidansu SARFRAZ* Mummy nagani tanata safa da marwa a falour ita kuma Nawaz tana zaune akan sofa tayi Tagumi, mum ce tace "wai meke faruwane ace mutum yafita daga gida tun karfe takwas batayiba ace yanzu karfe shadaya bai dawoba kuma nakira wayarshi ba'a dagawa. Nawaz tace "Allah dai yasa Yana Lapia ba wani abu bane ya faru, ameen" cewar mummy..... wayar mummy ce tahau kara, *@matarrrasheed**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 20* *✍🏻written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji "OUM AEYMAN"* *Supreme writers association, we write with the ink of era, that's era is our ink* Wayar mummy ce tahau kara, daukar wayar tayi a kidime domin number dad ce a gaban wayar ..... A kunne tasa ko sallama ta kasa yi.... Dad ne yace ASSALAMU ALAYKUM madam! Jikin mum ne yahau rawa tama kasa magana.... Nawaz ce tayi karfin halin Amsar wayar, "Assalamu alaykum dady mum tana bayi ne amma idan ta fito zan fad'a mata..... A'a Ashe daughter ce" to shikenan dama cewa nayi bari na Kira naji ko kun tafi? "A'a dad bamu tafiba, amma yanzu Insha Allah zamu tafi," OK to kudaiyi sauri domin garin akwai Nisa,, To daddy insha Allah, kashe wayar tayi tana kallon mumy wacce harta Fara zufa.... " Nawaz gaskiya kin taimakeni dabadon kin amshi wayarba to nidai bansan me zancewa abban nakuba" Nawaz tace "hmm mummy nima karfin hali Nayi, kuma ya kamata mu tashi mubi Sahu domin bamusan abinda ya faruba, domin ni nafara tsorata, yakamata ace ko ina yaje, Yadawo yanzu "hakane daughter, Amma kuma Bayan Haka Idan Mun fita ina zamubi? Kodayake bari nakira hajiyar naji yaje ya amso miki kayan danace, kinga idan yaje da sauki, idan kuma baijeba kinga akwai Matsala kenan..... number hajiya tayi dialing, Amma abin haushi wayar a kashe.... Number SARFRAZ ta kara Kira namma a kashe, wayar ta wurga Saman sofa sannan ta dafa kanta " oni karimatu nabanu yau, a Ina zan saka rainane, ya Allah ka nunamin yaron nan Don darajar annabi ....... Itama Nawaz duk tayi sukuku, tana tuna rashin lapiar dayayi, "aranta take cewa ko yana cikin tukin ne ciwon cikin nashi ya tashi Allahu a'alam........ *SARFRAZ* Juyawa yayi da nufin Gyara kwanciya, idonshi ya hango mishi wani irin labule.... Bud'e idon yayi sosai domin yanaso ya gane a Ina yake? Da sauri ya tashi zaune domin ya tuna duka abinda ya faru, Tunani ya Fara ya to ina ABDUL d'in, karfe nawa yanzu? Kuma nasan su mum suna gida suna ta faman jirana..... Wayan shi ya gani a Gefen shi, da sauri ya dauka, abin mamaki saiya ganta a kashe alhali shi a kunne ya barta..... Da sauri ya dauka Don ya kosa yaga ko karfe nawa! 12missed calls yagani kuma duka number mummy, time ya kalla 11:21am cewa Yayi haba dai daga d'an kwantawa, Inaga dai ba dai dai yake tafiyaba, d'ago da kanshi dazai Yayi tozali da agogon dake Ma'kale a bangon d'akin, shima dai sammakal 11:22am Da sauri ya dira daga katifar, "yau na shiga uku, mezancewa mummy kenan gashi tanata kirana..... wata dabara ce ta fado mishi, dialling d'in number mummy yayi.... ko kara d'aya bata gama yiba mum ta d'aga "hello SARFRAZ Allah yasa dai Lapia? Murya kasa kasa SARFRAZ yace mummy yau Allah ya taimakeni "kinsan yanzu na bar banki saboda tsabar layi kuma saida aka kusa zuwa kaina kudin ya kare, saida muka jira aka kawo wani.... Wata sassanyan ajiyar zuciya mummy tayi "to Alhamdulillah yanzu Maza ka tafi kasuwar ka siyo kayayyaykin tsarabar. Ni kuma yanzu zan fita naje gidan hajiya Bilki in amsowa nawaz nata, kaga ka huta kada abin yayi maka yawa...... Cewa sukayi to, sannan ya kashe wayar Yana hamdala a bisa saukin shawo kan mummy dayayi .... hulanshi ya dauka yasa sannan ya karasa mirror ya Duba fuskarshi, Takalminshi ya dauka yasa sannan ya duba mukullin motar ya dauka, bud'e kofar Yayi ya fita sannan ya maida ya rufemai Harya shiga mota baiga kowaba, hakanan da sauri ya nufi super market, a hanya yanata tunanin wacce zashi wadda sukeda POS basai ya tsaya banki ya ciro kudiba, SABODA yasan akwai layi tunda anyi salary... sahad ya wuce, nan ya ciro list d'in da mummy ta bashi, Haka ya Fara yawo Yana za'ba, sai faman kwaso kaya yake yana jibgawa a shopping chart, wasu masu siyayyar har tsayawa suke suna Kallonshi.... shikuwa SARFRAZ damuwace ta kamashi domin wani irin mugun barci yakeji Wanda baisan dalilinshiba ...... Dakyar ya gama siyayyar, master card d'in ya mika musu su ciri kudin, domin ko magana baya sonyi, receipt suka mika mishi had'e da master card d'in, Amsa yayi ya shiga mota ya bud'e seat d'in baya domin kayan sunfi karfin boot...... Dakyar yake tukin domin jinshi yake Kamar Bai ta'ba barciba a duniya, Haka yayita tukin ganganci harda masu zaginshi, . tsarewar Allah ne kawai ya kaishi gida, yana bude motar ya fita baima tsaya ya rufeba Yayi parlour, Nawaz idonshi ya ganin mishi zaune a kasan carpet...... da sauri ta Mike "SARFRAZ ka dawo? eh kawai ya iya ce mata, nan ya zube a gefenta "kaina yana mini ciwo " yana gama fad'an Haka Sai barci kuma da alama mai nauyi ne..... zama tayi dirshan tana mamakin meyasamu SARFRAZ da safennan....... bata kaiga ba kanta amsaba sai ganin mummy tayi a gabanta, ledojin hannunta ta ajiye a gefe, "nawaz naga kin tasa SARFRAZ a gaba ne, meya faru? Nawaz tace mummy babu komai, Yadai shigo a gajiyene shine yace kanshi Yana ciwo sannan ya kwanta anan, Daria mum tayi, nawaz kenan, kinsan SARFRAZ bayason hayaniya, Inaga layin bankin dayabine da kuma siyayyar da Yayi su suka haddasamai ciwon kan, yanzu ki barshi zuwa mu gama shirya komai Insha Allah ciwon kan zai sakeshi, tashi mujé mu had'a kayan, Mikewa Nawaz tayi "to mummy...... driver tasa ya shigo da kayan cikin motar, sannan ta shiga bedroom dinta ta kwaso leather boxes guda uku...... Kaya tayita faman zubawa a ciki, saida ta cika guda biyu sannan ta tashi ta shiga d'akin SARFRAZ ta dauka wani akwatin shima anan Ta cikashi da kayan SARFRAZ..... . Dayan shima ta cikashi da ragowar atampopi da sabulun..... Itadai Nawaz sai abinda mumy tace tayi takeyi..... Sai around 12:33pm suka gama had'a komai Amma har lokacin SARFRAZ bai tashiba.. nawaz kuwa tuni tayi wanka ta shirya, mum ce ta tasheshi SARFRAZ SARFRAZ katashi mana waiko barcin mutuwa kakeyine? dakyar ya bude idonshi, ya tashi yanajin idon yayi mishi nauyi, dakinshi ya nufa donyin wanka...... Yana shiga wayarshi ta fara kara, Dubawa yayi yaga Ashe ABDUL ne..... yana dagawa ya Fara masifa haba abdul menayi maka ne, saika tafi ka barni Ina barci maimakon ka tasheni sanda zaka fita..... Maganganun da ABDUL yake fad'a mishine sukasa ya saki wayar a kasa bai shiryaba "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un yake ta faman maimaitawa "nashiga uku, no wonder na zama Kamar mahaukaci sai barci nake babu fullstop ba coma. kubiyoni donjin me ABDUL yacewa SARFRAZ *MATAR RASHEED**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 21* *✍🏻written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji* *supreme writers association (SWA)* No wonder sai barci nakeyi babu fullstop ba coma.. Amma kuwa Fatima bata kyauta min ba wallahi. Nawaz ce ta shigo "Assalamu alaykum mummy tace na Duba Wai koka gama shiryawa, Cewa Yayi "malama kimini jaje don Allah.... Nawaz tayi murmushi "jaje name pah? Fuskar tausayi SARFRAZ Yayi "Dana fita daga nan gidansu ABDUL na fara zuwa, anan ya kawomin tea da doya.... Ashe acikin ruwan tea d'in kanwarshi ta zuba kwayoyin sa barci guda biyar wai saboda yasha yayi barci saboda baya iyayin barci.... Mu Kuma bamu saniba nasha, gamu da tafiya a gabanmu.... Yanzu yaza ayi kenan. Nawaz tace kada ka damu kai dai yi sauri ka shirya.... Mummy ce ta fara kwala mata Kira *Nawaz Nawaz, Amsawa Nawaz tayi "Na'am mummy ganinan Yana wankane be fitoba... Da sauri ta fita zuwa wajen mum, Mum ta kalla tadanyi murmushi "mumy ba dazu driver yace zai tafi jigawaba, shine nace don Allah idan be tafiba mu tafi tare, kinga Sai ya rage mana hanya... Banaso tukin yayiwa SARFRAZ yawa,. Dad'i mummy taji ganin Nawaz ta nuna damuwarta akan SARFRAZ d'in..... "to daughter kada ki damu bari nayi mishi magana, Mum na fita naw6az tayi d'akin SARFRAZ Da gudu, cikin rashin Sa'a ta samu ya shiga wanka,,, fitowa tayi tana jin dad'i zataje taga ummin ta. umma ce ta fado mata "oh koya jikin umma Oho, gaskiya ta maru domin SARFRAZ bai sassauta mataba.... dai dai nan mummy ta shigo tare da driver, Akwati biyu ya dauka ya fita, Nawaz ta dauki d'aya zata bishi, nan mummy ta hanata "haba naywaz kin manta Bakida Lapia ne, ki bari yanzu zai gama, idan sarfraz ya fitoma zai tayashi kinji..... "to Nawaz tace sannan ta samu guri ta zauna..... *GIDANSU NAWAZ* umma nagani ta tasa fauziyya a gaba "wallahi fauziyya idan baki samomin bokan dazai sa nawaz tabi duniyaba wallahi zamu raba jaha..... tun tuni sai kashe kudi nake a banza, aiki bayayi, yanzuma ji rashin mutuncin da aka mini kuma ta sanadinta... Amma ko abin ya dameki ki tashi tsaye. fauziyya tace "umma kiyi hakuri don Allah, kuma kibani kwana biyar saina nemo mana hatsabibin boka aduk inda yake...... umma tace na baki amma ki tabbatar aikinshi Kamar yankan wuka yake.... to umma zan ƙoƙarta cewar fauziyya tana Mikewa "bari naje gida mamarshi zatazo yau, kada tazo bananan kinsanta da gulma donma a tsaye nake.. .. to ki tafi Amma idan ta tafi ki dawo...... *SARFRAZ* ya shirya Tsaf ya fito amma daka ganshi zaka gane akwai damuwa a tare dashi, fitowa gurin mummy yayi. "mummy na shirya, gashi kuma kaina ciwo yake dakyar in zan iya yin tu'kinma,... dariya mummy tayi "SARFRAZ kenan, ai Bakada matsalar tuki, domin y'ar uwar ka ta nemar maka sau'ki, tace driver ya kaiku jigawa inyaso sai Kai ka karasa daku Maidugurin, Murmushi yayi "Allah sarki malama Inaga ta gane banajin dadine, Murmushin mummy takuma yi "uhm kundaifi kusa..... cikin y'an minute har an had'a komai, Suma sun shiga motar. mummy ce tsaye a gaban motar tana yi musu addu'a, Nawaz harda y'ar kwalla, shikuwa SAFyRAZ ya jingina kanshi da Kujera..... fita sukayi daga gidan, sai sannan mummy taji kwalla na neman cika mata ido, saboda ta saba da SARFRAZ ga kuma naywaz itama akwai shiga rai....... Haka ta koma parlour ta zauna tayi shiru....... Shikuwa driver direct yadauki hanya, tun ba'ayi nisaba SARFRAZ ya Fara barci, itama nawayz dama irin masu barci a mota ne..... SARFRAZ baifi minti goma da Fara barciba itama ta fara gyangyadi.... ganin sunyi Kusan awa d'aya suna tafiya driver yace.... Yallabai ko akwai abinda zaku siya, domin mun kusa fita daga gari, kunga babu damar tsayawa kenan koh? shiru driver yaji, hakan yasa ya waigo.. murmushi yayi ganin Nawaz a Saman kirjin SAFRtAZ sai faman sheka barci sukeyi.... ohh nifa har yanzu na kasa sanin meye alakar wannan yarinyar da SARFRAZ domin nidai ance shikenan d'an d'an su hajiya...... Kila ita zai aura kuma.... share zancen yayi yaci gaba da tukinshi. *misalin 4:23pm suka Isa Kano* Anan driver ya samu guri Yayi parking domin tayarsu ta sace..... me Gyara ya nemo, daya Duba ya sanar mishi cewa sai an chanza tube saboda bazai liƙu ba domin ya ɓuɓɓule..... kudi ya bashi domin yaje ya siyo.... shi kuma ya koma motar Yana tunanin irin wannan barci nasu SAyFRAZ.... Saida aka kwashi kusan rabin awa d'aya sannan Mutumin ya dawo da tube ɗin yake fadawa driver cewa dakyar ya samo..... nan suka kwance taya suka fara gyara..... SARFRAZ ne ya bud'e ido, ganin Nawaz yayi kwance a kirjinshi hani'an sai barcinta takeyi..... murmushi yayi "itama wannan ta kamu da ciwon barcin kenan... ganinsu yayi su kadai babu driver, glass ya sauke, anan ya hango driver da bakanike, driver ya Kira yace "Lapia meya faru? Ehm dama tayarce ta samu Matsala shine ake chanza tape yanzu hakama Muna kano unguwa uku..... Cewar driver SARFRAZ yace "babu komai ku natsu ku gyara dakyau... wayarshi ya dauko Don kiran mummy nan yaga missed call dinta yafi ishirin, da sauri yayi dialling din number. kara biyu ta dauka "haba handsome meya faru inata Kira kunki dauka kunsa duk hankalina ya tashi.. kasa Yayi da murya "mummy kiyi hakuri wallahi dukanmu barci mukeyi, yanzuma natashi ni, ita kuwa bata tashiba.... Mum tace to shikenan babu Matsala, toya hanya? Nasan yanzu kunkai jigawa koh. A'a mummy bamukai jigawaba har yanzu Muna kano motarce ta samu Matsala.... da sauri mummyn tace Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un, meya faru? Mum ki kwantar da hankalinki tube kawai ake chanzawa ba wani abu bane..... Sai sannan Tayi hamdala tace to anjima zan kira inji ko an gama gyaran, sannan ta kashe wayar.... tashi Nawaz tayi a kirjin SARFRAZ "nifa kaga banason iskanci yazaayi don Nayi barci saika wani janyoni kirjinka ka rungume..... mamakine ya kama SARFRAZ "nine na rungume ki, kecepah kika rungumeni wallahi... muɗimuɗi tayi da rai, nifa iskancinka ya Fara isata Allah..... Nawaz nine d'an iska? Kallonshi tayi dakai meye inba dan iskaba? yaji zafin maganar amma saiya basar. driver ne ya zagaya ya shiga motar yace yallabai angama gyaran, nawane cewar sarfraz. A'a oga Aina biyashi. Nan suka dauki hanyar jigawa Misalin shida saura...... Haka suke ta tafiya har saida aka Kira magrib lokacin sun Isa gaya anan suka tsaya sallah amma banda Nawaz tunda batayi. tunda suka tashi a gaya suka tarar da goslow basu suka Isa dutseba sai Misalin takwas da rabi. anan sukayi sallama da driver yace shi birnin kudu zai wuce. babu Wanda yakeyiwa Dan uwansa magana tun fad'an da sukayi a Kano.... shiru SAyFRAZ Yayi, ya koma driver seat, A sahad ya tsaya yashiga ya siyo ice-cream da yoghurt. nan ya karasa gurin mai nama ya siya musu steam chicken. cikin dutsen ya shiga yanata dube dube, nan ya hango wani guest inn. Karasawa yayi, ya fita anan ya Samar musu d'aki aka bashi key. dawowa Yayi kifito muje, bata kulashinba ta fito, shi kuma ya dauki ledoji yayi gaba tana biye dashi. a falour Ya zauna yace mata tazo taci abinci, Cemai tayi to bari nayi wanka sannan ta shiga ciki tasawa kopar key. sai Bayan minti ishirin ta fito sanye da doguwar Riga ta yafa gyalenta. Kallonta yayi ya mika mata ledar, tana ci tana cika tana batsewa Sai Kace mecin magani.... dariya yayi a ranshi zanyi maganinki ne yarinya.... tashi Yayi shima ya shiga ciki yayi wankan ya fito dagashi Sai gajeren wando... Harararshi tayi ta tashi ta shige ciki harda sa key murmushi SARFRAZ Yayi Wanda shi kadai yasan maanarshi.... Bayan Kamar awa d'aya, goma saura kenan, sarfraz naga yasa key ya bud'e bedroom d'in, ciki ya shiga ya mayar ya rufe a hankali, hajiya Nawaz na kwance anata faman barci, da wata yar yololuwar Riga. kan gadon ya karasa ya dauketa ya d'ora a Saman cinyarshi bakinshi ya had'a da nata Ya fara sumbatarta, baabu shiri ta tashi daga barci, ihu ta fara amma babu hali saboda ya rufe bakinshi da nata, Sarfraz kuwa cewa Yayi "nine SARFRAZ d'an iska, nazone na nuna miki iskancin nawa ki ganshi ra'ayil aini... ihu ta fara don Allah kayi hakuri wallahi wasa nake maka cikin shakakkiyar murya.... cewa Yayi "bansan wannan ba ya dad'a hade bakinsu guri d'aya..... Toh masu karatu ku biyoni donjin wace waynar SARFRAZ zai toya *MATAR RASHEED**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *episode 22* *🤳written by Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji (Oum aeyman)* *Supreme writers association (SWA)* *We write with the ink of era, that's era is our ink* *We satisfy entertain and touches our readers mind* Cewa Yayi bansan wannan ba, ya dad'a had'a bakinsu wuri d'aya...... Shure shure nawaz taketa faman yi tana kokarin kwace kanta, amma takasa ko kwace hannunta.... Iya ko'kari tayi naganin ta kwaci kanta Amma ta kasa, hakan yasa kawai ta fara zubar hawaye tunda babu ba'kin magana..... Sunfi minti goma a haka, sannan SAFRAZ ya saketa...... Jikinta Sai rawa yakeyi tana zazzare ido.... D'an guntun murmushi yayi "naga Kamar akwai magana a bakinki? Cikin sauri tace "Eh wallahi.... Kallonta yayi "to fad'i muji meye, Cikin hawaye tace "Don girman Allah, Don darajar alqur'ani ka kyaleni kada kayi mini komai Don Allah..... " Kuma koda nace maka Dan iska wallahi wasa nake maka, ba Haka nake nufiba.... "Domin kaf duniyarnan ban ta'ba ganin mai kyawawa Hali irinkaba..... "Hmm Idan kika kumafa? Cewar safraz yana Kallonta "wallahi idan na kuma kayimin abinda yafi wannan,, d'aga gira yayi "Haka kikace koh, to na yarda.... Sauketa yayi daga jikinshi sannan yace "kwanta kiyi barci domin gobe da wuri zamu dauki hanya...... Jikinta sai rawa yakeyi, gaba d'aya ta rasa natsuwarta ... Kallonta yayi, sannan ya fita daga d'akin ya koma parlour,, jallabiya yasa ya dauki duvet ya kwanta a Saman sleeping couch ya rufa, Sai dariyar zuci yakeyi saboda nawaz ta bashi Daria sosai.... ooh wato nawaz harta yarda cewa zan iya yi mata wani abu kenan? hmm batasan nima karfin Hali nayiba, Ashe itama muguwar matsoraciyace naketa wahalar da kaina.... Kuma cewa Yayi "ya Allah ka karemu da son zuciya da aikata aikin dana Sani.... Yana wannan sake saken barci Yayi awon gaba dashi. ita kuma nawaz tana nan inda ya barta ko kwakwkwaran motsi ta kasayi, domin gani take zai dawo. tafi minti ishirin a haka sannan ta tashi ta bud'e fridge ta dauki ruwa Tasha, kwantawa tayi taja bargo ta rufa..... har lokacin jikinta rawa yake, tafi awa daya a kwance Amma fir barci ya 'kauracewa idonta..... Haka dai tayi shiru ta sa'ka wannan ta warware, tana rokon Allah yasa safiya tayi har gajiya da kwanciyar tayi, amma barcin yaki zuwa, bata ankaraba saijin kiran sallar farko tayi, Tashi tayi ta shiga bayi tayi wanka ta dauro alwala Ta fito, Shiryawa tayi sannan ta shimpida praying mat Ta fara sallah..... Tana cikin sallah SAFyRAZ ya wuceta ya shiga bathroom d'in, wanka yayi Yayi alwala sannan ya fito.... Jin fitowarshi yasa nawaz ta Mike tayi Kamar bata idar da sallar ba domin bataso ko magana ta had'a su.... wucewa yayi ya koma parlour, Bayan ya shirya ya fita zuwa masallaci..... Tanajin fitarshi Ta cire hijabi ta hau Saman gado Ta zauna... mudubi ta dauko ta duba bakinta, gani tayi Yayi ja Kamar jini zai fito..... Tsaki tayi "Mtswess Allah ya isana, kuma bazan yafeba. mugu kawai kuma ance Dan iska, kayi abinda zakayi *(Nidai OUM AEYMAN cewa nayi Aida kinbari Yadawo saiki fad'a a gabanshi)* Cewa tayi mutum sai karfi Kamar babu jini ajikinshi, nidai Allah ya rabamu lapia tana dada jinjina irin tsaurin iso da rashin kunyar da sarfraz yake nuna mata.... da ace jiya yamini wani abu dana shiga uku na lalace..... yanzuma lallabashi zanyi mu rabu Lapia..... Komawa tayi ta kwanta, kasan cewar batayi barciba da dare yasa tana kwantawa yayi gaba da ita.... shi kuma SAFRAZ Bayan an idar da sallah bai fito daga masallaci ba, zama yayi ya dauki alqur'an yana karantawa.... bashi ya fito daga masallacin ba saida gari yayi haske... reception yaje Yayi musu order d'in breakfast, sannan ya koma d'aki.... Jin shuru shuru yasa ya shiga bedroom d'in, ganinta Yayi tanata faman barci hani'an...... d'an Jan hancinta Yayi, firgitgit ta bud'e ido, ganin SARFRAZ yasa ta kauda Kai domin Jitayi tanajin kunyarshi bazata iya kallon cikin idonshiba.... zamewa kasa tayi "Ina kwana yaya sarfraz? dariya yaji tazomai, amma saiya bone, lapia lau kanwata Ina Fatan kin tashi lapia.... cewa tayi Lapia lau.... kanne mata ido yayi had'e da d'aga mata gira "toya gajiyar jiya, kuma Ina fatan an yafe mini? Cewa tayi niban gajiba.... in a questioning manner ya kalleta, baki gajiba pah kikace? to bari a mai maita, Da sauri nawaz tace nifa ina nufin na yafe makane..... dai dai nan bell d'in kopar tayi 'kara tashi Yayi I'm coming. Yana fita tace jishi Kamar wani salihi, amma iskancine fal cikinsa.... dawowa Yayi rikeda abincin da yayi order, Take away biyu ya mika mata da plastic cup... Amsa tayi ta bud'e takeaway d'in ganin plantain chips da Irish tayi .... Shikuma cup d'in tea ne aciki mai zafi.... Ahankali take ci, bata wani ci dayawaba tace ta koshi, bai matsa mataba yace to yanzu ki had'a kayanki sai mu tafi koh? kayayyaykin data ciro Daga cikin akwatin ta kwashe ta mayar.... sannan tasa hijab, Karasawa tayi ta tarar shima ya gamaci, "nashirya tace ta tsaya " cewa Yayi to sannan ya kwashi abinda zai kwasa ya fita tana biye dashi, reception ya karasa ya basu mukullin, sannan ya wuce parking lot... motar ya bude ya shiga driver side, itama gudun magana yasa ta shiga daya side d'in.... igniting motar yayi suka fita daga guest inn din suka dau hanya..... suna cikin tafiya ya tuna bai kira mummy ba kuma itama bata kirashiba.... wayarshi ya dauka yayi dialing d'in number, ji yayi a kashe.... sai sannan Ya tuna da wayar daya siyowa nawaz, hannu yasa a locker din motar ya ciro kwalin waya, mikawa nawaz yayi ga wayarki, sannan ya mika mata SIM card gashi kisa inyaso saiki kira su ummi ki fad'a mata Muna jigawa.... yi tayi Kamar bazata amsaba, sai ta tuna yanda sukayi.... ansa tayi to nagode sosai... bud'e kwalin tayi ta ciro wayar, kwalin ta kalla taga iPhone 13 pro shiru tayi tasa SIM card d'in, number umminta tayi dialling, ta can bangaren ummi ta daga "Assalamu alaikum" Cikin farinciki nawaz tace ummi nice, Ina wuni. da sauri tace "nawaz kin tayar mana da hankali wallahi, munata zuba ido jiya Amma babu Ke babu alamunki..... "Ummi kiyi hakuri yanzuma na kirane na fad'a miki Muna jigawa..... Au Ashe kun kusa, to Allah ya kawo ku Lapia.. nawaz tace ameen ummi.... binta yayitayi da kallo, Yana murmushi.. cewa tayi meye kuma?.... daure fuska yayi Yayi parking yace ya mukayi dake....... da sauri tace ai bana nufin komai Allah..... Kallonta yayi yace to me kike nufi.... "Nidai Dan Allah kayi hakuri.. Murmushi yayi yaci gaba da tafiya. Tunda suka dau hanyar Azare titin shiru babu ko motar daya, tun Basu luraba har suka lura. "Yaya sarfraz wai ya naga titin shiru ba alamun kowa? "Mtsewwwss wallahi Nima tun dazu nake mamaki ace babbar hanya kamar wannan data hada garuruwa da yawa Amma babu kowa sai mu kadai, Anya kuwa lafiya? Karar Harbin da suka jine yasa sarfraz taka burkin da bai shiryaba , dukansu Saida sukayi gaba sannan sukayo baya saboda yadda yake tafiya in a high speed. Tsorone karara ya bayyana a fuskar Nawaz har zuface ta tsatstsafo mata a goshi tsabar firgici. Shima sarfraz ya firgita Amma dayake namiji ne sai bai nunaba "Nawaz ki nutsu insha Allah babu abinda zai faru. "Hawayene ya fara zubowa a fuskarta "sarfraz idan wani abu ya sameka bazan taba yafewa kainaba har abada saboda dalilina ka tawo garinnan nasan ba don ni ba da babu abinda zai rabo ka da ahalinka. Kureta yayi da Ido Yana tunanin wani abu "look Nawaz nace ki nutsu insha Allah ban....... Mutane suka gani sun nufosu da gudu wasu a kasa wasu a mota suna yin reverse. Wasu mutane ne daban rike da bindiga duk fuskarsu rufe da rawani suma biye dasu suna Harbin me kan uwa da wabi. Zunduma ihu Nawaz tayi "innalillahi wa'inna ilaihiraji'un sarfraz mu fita muma mu gudu kaga kowa gudu yakeyi. Hannunta ya rike dukda Shima a razane yake "calm down Nawaz babu abinda zai faru face abinda Allah ya riga ya tsara, ko mun fita mun gudu kafarmu Bata Isa ta wuce kaddararmuba . Rufe bakin shi Leda wuya wani rike da bindiga ya Bude kofar motar "ku fito shaidanu" ya fada Yana nuna Nawaz da bindiga. Bb"Dan Allah kada kayi mata komai" cewar sarfraz cikin tashin hankali. Nawaz da gaba daya ta jike da zufa tsabar tsoro da fargaba tace "Nidai ko menene kamini Amma shi ka kyaleshi wallahi nice silar zuwanshi Nan. "Oh wato ku ga masoyan asali kowa baiso a kashe Dan uwanshi" ya fada cikin wata kakkausar murya mara Dadi Harbin sarfraz yayi a kirji sannan ya nunawa Nawaz wadda tuni ta fara zunduma ihu bindiga a kanta "fita muje ko kema na fasa Miki kwanya Ko da dai nasan Zaki iya Yi mana amfani ko dare ma rage Dake Taso tayi gardama Amma ganin yanda sarfraz ya Dage Yana nuna mata alamun ta bishi yasa ta fita daga motar hannunta a Sama. Ganin yanda gurin da aka Harbi sarfraz yake Jini yasa Nawaz ta Kara zunduma wani ihun tana tsalle " nashiga uku me zancewa mummyn sarfraz? Shikenan sarfraz zai mutu sabodani? Kan bindigar ya buga mata a gadon bayanta "don uwarki wuce muje" tsabar azabar da taji yasa ta nemi kukan da take ta rasa idonta Shima ya kekashe. "Koma mezai faru saina rayu ko don narika yiwa sarfraz addu'a" ta fada a zuciyarta Gurin wasu gungun mutane Maza da mata ya nufa da ita, kowa hajaran majaran ana kadasu kamar dabbobi wasu daga gefe kuma suna harba bindiga a iska. Tafiya suke suna ratsa cikin daji ga uwar ranar da akeyi, wasu har faduwa sukeyi Amma haka za'a buga musu bindiga su kuma mikewa. Tuni zuciyar Nawaz ta bushe tana tunanin ai yanzu sarfraz ya riga ya mutu duba da yanda Taga Jini na zuba a jikinshi dazu. Sun kwashi kusan awa hudu suna tafiya a daji inda daga bisani suka isa wasu rukunin bishiyoyi da duk bukkace a kasansu. Wasu tarin Yan bindigar ne a gurin wasu na zukar taba wasu na zuba bullet a bindiga wasu kuma a kishingide. Harbin bindigar da aka saki a iskane ya dad'a razanasu "kowa ya samu guri ya zauna " cewar Wanda ya harba bindigar A rude suka zazzauna inda wasu kwantawa sukayi tsabar kishirwa da yunwa. Dai dai da dai dai Nawaz ke bin kowa da kallo, sunfi au hamsin Amma yawanci mazane sukafi yawa matan basufi su Tara ba. Idon Nawaz ya sauka kan wata mata me tsohon ciki , sai murkususu takeyi ga bakinta daya bushe yayi fari wani tsoho ne gefenta akalla zai haura shekara saba'in Wata Cristian ce a gefe ta rufe Ido hannunta a hade tanata magana ahankali Girgiza Kai Nawaz tayi "la haula wala quwwata illah Billa, wannan wane irin bala'ine? Numfashin wani matashin saurayine Wanda daka kalleshi zaka gane Dan masu hannu da shuni ne duba da sururar Dake jikinshi idonshi yayi ja bakinshi a bushe alamar ya gama tagayyara "La haula wala quwwata illah billah, innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, Allah kaga halin da muka tsinci kanmu aciki ya Allah Kaine Allah ka kawo mana mafita, Tuna uban mutanen da suka harba tayi Wanda daga cikinsu harda sarfraz da ke can batasan halinda ke ciki ba. "Babu Wanda zan dorawa laifin mutuwar sarfraz daya wuce umma, tunda da Bata turo amini fyade ba babu abinda zai sa nafita daga gida har mu hadu da sarfraz. Amma Allah shine me kowa Mai komai kuma insha Allah saiya biwa sarfraz hakkinshi. Harba bindigar da akayi a samane ya dawo da Nawaz daga tunanin da takeyi. Wasu ta Gani sun ajiye cemata a Saman wani table me tsawo " ku kallemu Nan munafukai" daya daga cikinsu yace Yana gyara camera saitinsu Nawaz , fara magana yayi "Sako zuwa ga gwammatin tarayya, wadannan mutanen da kuke Gani sune wadanda muka tare a hanyar Azare zuwa Maiduguri, inaso shugaban kasa ya Bude kunnenshi da kyau yaji abinda zance, "Indai kunaso asaki wadannan mutanen su koma cikin iyalinsu to sai an tanadar mana da kudin da za'a fanshe su naira biliyan goma. Inba hakaba gobema zamu wani gurin mu Kara tare wasu. Dariya ya kyalkyale da ita sannan sukayita harba bindiga a iska daga bisani suka kashe camerar. Daga Mai kuka sai Mai ihu sai masu salati da cewa Jesus, Jin yawan kudin da ake bukata kafin a sakesu Duk sun fidda Rai don sunsan gwamnati bazataba Yan ta'adda wadannan makudan kudin ba. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sarfraz na ganin sunri nisa ya samu duster din dayake goge cikin mota da ita yasa a kirjinshi ya danne Jinin daketa zuba, Shi dama burinshi kada a harbi nawaz yasan insha Allah Allah zai kawo mafita Koda an tafi da ita. Fita yayi daga motar ya nufi cikin daji Yana tafiya Yana raba hanya sanadiyar jirin daya ke dibarshi saboda yawan Jinin daya zubar... Dena Gani yayi sanadiyar duhun daya ziyarci idonshi sai ji yayi ya fada akan wani abu Mai uban karfi be ko kuma shurawa ba To masu karatun kunji iftila'in daya faru dasu Nawaz Ko Allah zai kawo musu mafita Oummou muhsien ✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 23* *_Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji_*✍️ Zaune Nawaz take ta saƙa wannan ta warware, bata taɓa tunanin rayuwa zata juya mata baya hakaba acikin ɗan kankanin lokaci. Kuma nadamarta bata wuce da tasan haka zata faru da duk yanda za'ayi bazata yarda Sarfraz ya biyo ta ba... Pure water aka basu kowa guda ɗaya "ga ruwa nan kuyi duk abinda zakuyi dashi don shine abincin ku na yau. Shiru Nawaz tayi tana tunani "Gara nayi alwala da ruwan nan idan yaso sai insha wanda ya ragu. Gefe ta samu tayi alwala, suma sauran mutanen ganin tana alwala yasa suma suka farayi. Ɗaya daga cikin Mutanen da suka sato su ta kalla "don Allah inane Gabas? Nuna mata yayi da hannu , juyawa tayi ta kalli inda ya nuna mata ta tada kabbara. Tayi raka'a biyu wani shima sanye da rawani ya ƙaraso gurin, ganin yawancin mutanen suna sallah, taɓe baki yayi ya kalli wanda ke gefensu a tsaye yace"kai iluu kana tsaye ka bari suke sallah saboda suyi addu'a Allah ya tona mana asiri koh? "A'a oga naga ai sallah sukayi ba wani abuba, kuma idan na hanasu yin Sallah Ai aikinmu zai iya ɓaci. Sigari ogan ya fito da ita yasa lighter ya kunna sannan ya fara zuƙa, bai cewa iluu komaiba ya wuce gaba. Dai dai nan Nawaz ta idar da sallar,. Jingina tayi da bishiya tanata addu'a a cikin zuciyarta. Shi dai iluu sai kallonta yakeyi, tun sanda aka kawosu dajin yaji ta burgeshi gashi tana mai yanayi da kanwarshi.. Ji yayi anya zai iya bari ayi mata wani abu kuwa? Dan kusa da ita ya matso ya fara magana a hankali "sannu baiwar Allah, kinajin yunwa ne? Mamaki ne ya kama Nawaz ganin har wani ya damu da halin datake ciki, taso ne tayi banza dashi to amma ko babu komai ya nuna ya damu da ita kuma ko bahaushe ma yace ka gaida mai gaida ka. A hankali tace "yauwa sannu, banajin yunwa sai dai gida da nakeso naje, Shiru yayi bai kuma yin maganaba ya matsa daga kusa da ita, Ita dai Nawaz sai addu'a takeyi a cikin zuciyarta musamman ma _ALHAHUMMA AJURNI FI MUSIBATI WA AKLIFLI KAIRAN MINHA_ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Wasu yan Fulani ne tafe da shanun su, da alamu sun dawo daga kiwo ne, Mace da namiji ne dukkanin su bazasu haura shekara goma sha uku zuwa sha huduba. Har sun gifta macen ta dawo baya saboda taga kamar mutum kwance, ile kuwa ganin sarfraz tayi kwance shame shame ko numfashi bayayi. Cikin razana tace "bandi ware" Wanda ta kira da bandi ɗin ne ya karasa kusa da ita cikin hanzari. Shima zare ido yayi ganin mutum kwance baya motsi... Tsugunawa yayi yana tattaɓa sarfraz ɗin don ya gane yana raye ko ya mutu. Pulse ɗin shi ya taɓa cikin Sa'a kuwa yaji tana bugawa a hankali. Kallon macen yayi yace "hassu bata mutuba mu kaita gidanmu che mu mata magani kinga batada jini kuma harbinta akayi, idan muka barta anan mutuwa zatayi. Cikin Hausar ta dake nuna ita ɗin tsantsar fulanice tace "bandi taya zamu iya daukan ta? "Ki kama min ita mu ɗora ta akan gwalbo, "To" cewar hassu tana yiwa wani sa tsawa, Aikuwa chak san ya tsaya ya natsu duk da yan uwan shi na tafiya amma be bisu ba, Da kyar da suɗin goshi suka daura sarfraz akan san sannan suka kuma mishi magana . A hankali ya ci gaba da tafiya yabi hanyar da yan uwanshi suka bi . Basuyi tafiyar minti goma sha biyar ba suka Karasa wata bukka mai dan girma. Chan wani fili mai fadi shanun nasu suka karasa suka kwakwkwanta, shikuwa gwalbo (san daya dauko sarfraz) kofar bukkar yaje ya tsaya Yanzun ma da kyar suka saukeshi, sai sannan gwalbo yaje kusa da yan uwanshi ya kwanta shima. A saman gadon kara suka dora shi sannan bandi ya fadawa hassu abinda zataje cikin daji ta samomai. Bayan ta tafi ne ya yaga rigar sarfraz saboda ya duba ciwon sosai, wani ƙaramin karfe yasa ya janyo harsashin da karfi, cikin Sa'a kuwa ya fito da shi. Wanke harsashin yayi sannan ya bude saman shi garin dake cikin harsashin ya barbada a jikin ciwon. Saida sarfraz ya motsa sai kuma ya daina motsi, Hassu ce ta shigo rike da ganyayyaki da sassaken ice "bandi gashi" Amsa yayi ya dudduba sannan ya mika mata sassaken yace taje ta jika shi a cikin ƙoƙo. Shi kuma ya samu dutse ya daddaka ganyayen sannan ya samu ƙoƙo ya zuba a ciki. Man shanu a tsiyaya akai sannan ya chakuda hade da mutstsika ganyen,. Ɗebowa yayi ya zuba a cikin ciwon yana dannanwa a hankali sannan ya mike ya fita daga cikin bukkar ya nufi inda shanunsu ke kwance. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Nawaz dai ta sadakar cewa sarfraz ya mutu, domin yanda takeji a zuciyarta da ace zatayi kuka da taji daɗi amma ta kasa shiyasa bahaushe yace kuka ma Rahma ne. Garin ne ya fara yin duhu alamun magrib ta Kunno Kai Iluu ne ya karasa kusa da Nawaz cikin dabara yanda ba za'a gane suna magana ba yayi kamar bindiga yake gyarawa "baiwar Allah kin bani tausayi kuma kinyi kama da ƙanwata, inaso na taimakeki ki gudu gida kinji, amma sai dan anjima za muyi sallah to idan kikaga an fara sallar ki bi hanyar nan ki gudu zata kaiki har titi amma gaskiya da nisa dakyar in Zaki iya kuma dajin nan yanada hatsari sosai akwai yan fashi da yawa harda yan shan jini, kuma bamu kadai bane masu kidnapping ba. Kallon shi Nawaz tayi "Nagode Allah ya saka da Alkhairi, zan tafi a haka, nasan Allah zai tsareni Wata yar karamar roba ya bata wadda daga yanayinta zaka gane ruwa ne a ciki sai wata karamar wuka yace "ki gudu don Allah, dakinga mun fara sallah kada ki bari a ganki, idan suka ganki kasheki zasuyi. "Iluu" wani dake dan gabansu ya kira iluu cikin daga murya yace "mekakeyi anan? Gunshi iluu ya nufa hade da cewa "harsashi na zuba a bindiga. Daɗi da fargaba ne suka dirarwa Nawaz a cikin zuciyarta lokaci guda, daɗin zata kubuta sai kuma fargaban ya zataje ta samu sarfraz, cire takalminta tayi tasa wukar a kasan takalmin sannan ta maida takalmin dayake cover shoe ne. Tananan zaune taga sun fara alwala, Ita dai tana ankare so take su tada sallar ta feche. Aikuwa Saida sukayi raka'a ɗaya sunyi sujuda Nawaz tabi bayan bishiya a hankali.. Saida ta danyi nisa sannan ta ruga da gudu, gudu take iya karfinta bata samma inda take jefa kafar taba, tun tana iya ganin gabanta har ya zama ta dena gani alamun duhun dare ya sauka, Bata damu da duhun ba saima karfin gudun data ƙara. Tun tana iya yi sosai har ta koma sassarfa daga karshema tafiya ta koma yi saboda karfinta ya kare gashi bataci komai ba. Tana cikin tafiya tana tangadi taga an hasketa da wata irin fitila me uban haske Duk da irin gajiyar da damuwar da take ciki hakan be Hana hanjin cikinta juyawa ba tuna maganar da iluu ya faɗa mata akan dajin. Chak ta tsaya bata kuma ko motsi ba.. Saida hasken yazo daf da ita taga ashe gungun mazane sukayo kanta.. Wani ne yayi saurin riketa yana cewa "wallahi Ni na nuna muku ita don haka saina gama duk abinda zanyi da ita sai in baku ragowar. Babu wanda ya Musa mishi saima washe Baki da suke yi ganin irin tsarin halittar Nawaz. Fizge fizge Nawaz ta farayi akan ya saketa. Amma ko gezau be motsaba, Saida yaga abin nata da gaske ne sannan ya fito da yar karamar bindiga daga aljihun shi ya nuna mata "idan baki nutsuba zan fasa Miki kai. Natsuwa Nawaz tayi tana binshi kamar jela. Cikin wata bukka ya nufa da ita, suna shiga ya maida kofar ya rufe, ga mamakin Nawaz katifa ta gani a cikin dakin harda zanin gado. Ce mata yayi zauna, ai da sauri ta zauna Wata leda ya ciro a Cikin wani dan akwati madaidaici dake ajiye a gefen katifar. ledar ya buɗe, cikin mamaki Nawaz take kallo kajine gasassu sai fresh milk da dan abubuwan ciye ciye Tura mata gabanta yayi "gashi kici ki koshi saboda idan baki koshi ba zaki wahala, don nidin in na samu mace bana raga mata. Zuciyarta ce ta bada daram "wannan wane irin bala'ine, dana sani na zauna achan wallahi. Kallon ledar kawai take amma ta kasa ko kai hannunta. "Ke garama kici don ko baki ciba Ni saina ci. Kuma Ni ba'a min gardama, idan kuma kikace ke gardama zakimin ta karfin tsiya zanyi sannan in harbeki kowama ya huta. Aida sauri Nawaz ta fara tuttura naman a bakinta, Saida taci da yawa sannan tasha madarar, dukda batajin dandano tsabar tsoro da fargaba, bakinta Salam yake. Hannu yasa ya cire mata hijab din jikinta, ganin irin dirinta yasa shi Binta da wani irin mayen kallo yana murmushi. Hawayene ya fara zubo mata ga jikinta daya fara rawa kamar mazari. Janyo ta yayi jikinshi yana kokarin sa hannunshi cikin rigar ta. Kuka ta fashe dashi "don Allah nasan kai Musulmi ne, kuma nasan kasan zina Haramce don Allah kada ka keta min haddi. Shiru yayi bece mata komaiba, sai kuma ya mike zumbur. Wata jaka ya bude ya kwaso wrappers wrappers din yan dubu dubu ya dora a cinyarta sannan yace "wa'azin ki ya shigeni, yanzu ba zina zamuyi ba sunnah zamuyi domin wadannan kudin da kike gani sadakin kine. Kuma ga Dukkan alamu na lura ke ɗin budurwace bakisan namiji ba to saboda haka na miki alkawarin zanbiki a sannu bazan wahalar da keba kinji. Wani kukan mai ciwo Nawaz ta ɗada fashewa dashi. Shikuwa beyi wata wata ba ya janyo ta jikinshi yana rabata da kayan jikinta sai wuntsil wuntsil takeyi, ai gogan naku jin hannunshi a saman boobs dinta saiya kara tayar mishi da hankali, cikin wuntsil wuntsil ɗin da Nawaz take yi ne fitilar dake ajiye a gefen gadon ya fadi kasa ta mutu, take ɗakin yayi duhu. Duhun daya bayyana a dakinne ya daɗa tayarwa da Nawaz hankali shi kuwa gogan kamar kara mishi azama akeyi. Yanda yake matsa mata boobs yasa ta kara fashewa da wani Marayan kuka "na shiga uku Ni Nawaz wai meke shirin faruwa da nine? Ya Allah nasan kana kallon halin da nake ciki ya Allah ka kawomin mafita. Dago hannu da zatayi taji ta rike abu zungurere, nan take zuciyar ta ta dena bugawa Tasan idan mutumin nan ya tura mata wannan abun babu abinda zai hanata mutuwa . Shikuwa baima san me takeyi ba Gaba daya ya fita hayyacinshi sai wani birkita mata gashi yake yana wani shinshinata _*MATAR RASHEED*_✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 24* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Ƙuƙƙulle shanun bandi yayi sannan ya samo kwarya ya tatsi nono a jikin wata shanuwa mai sabuwar haihuwa. Ɗakin ya koma sannan ya samu ludayi yana durawa SARFRAZ a hankali, kaɗan ke shiga bakin sauran na zuba a ƙasa. Saida ya bashi da ɗan yawa sannan ya ajiye ragowar a gefe, abinda keba bandi mamaki shine jikin SARFRAZ ya saki gaba ɗaya babu alamar yanada rai amma kuma zuciyarshi na bugawa kuma idonshi a bude yake. Damuwa ce me karfi ta kamashi ya kalli hassu yace "hassu kinga duka jikinta baya motsi amma kuma bata mutu ba. "Nima tun dazu nake kallonta, abin ya mini kama da abinda ya samu babansu jauro fa. "Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, kana nufin kace mutuwar jiki ce ta sameta? "Eh " cewar hassu tana mai tabbatar mishi da abinda take nufi Zama sukayi kusa da SARFRAZ sunanta kallonshi ga wani tausayinshi daya kama su, Babu abinda SARFRAZ ke iya yi illah dai idonshi a buɗe yake kuma yana ƙiftawa. Hassu ce tace "gashi su Dada ba yanzu zasu dawoba, yanzu ya za muyi da ita? "Nima ban saniba, Amma muci gaba da kula da ita koh? " Eh" tace haɗe da yin tagumi. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Tunawa tayi da wukar da ilu ya bata, sai kuma zuciyarta tace "anya Nawaz zaki iya kashe mutum? Tunani ta fara yi "ba kashe shi zanyi ba kwatar kaina zanyi, da inbar mugu, azzalumi irin wannan ya kwanta dani Gara na mutu kawai. Kuma Alamu ya nuna ya saba da zina ma, ƙilama har ciwo gareshi, kuma inje tsautsayi yasa in samu ciki, subhanallah, ji tayi zuciyar ta kara karfi akan ta ciro wukar kawai koma me zai faru ya faru. Kafarta ta ɗaga sama sannan a hankali ta zame takalmin kafarta, ta ciro wukar. Yunkurin mayar da ita kasanshi ya fara yi don yakai gejin da bazai iya resisting ba. Aikuwa cikin azama Nawaz ta Chaka mishi wukar a saitin marar shi inda dayan hannunta yake. Wani irin ihu me karaji ya saki tsabar azabar data ratsa mishi ƙwaƙwalwa, hankaɗe Nawaz yayi gefe yana neman ta yanda zai cire wuƙar. Hannu yasa ya taɓa wukar da niyar cirewa take wata azabar ta kara ratsa mishi cikin ƙwaƙwalwa.. Ihu ya ƙara saki ya fara laluben inda ya ajiye bindigar shi, don bazai barta ta gudu ba sai dai ayi mutuwar kasko. Ita kuwa Nawaz sai lalube take ko zata samu abinda zata rufe jikinta. Ji tayi ta taɓa zanin gado, ai da sauri ta janyeshi ta ƙudundune jikinta dashi. A hankali take tafiya tana laluben hanyar kofa cikin Sa'a kuwa taji ta taɓa kofar, cikin azama ta bude kofar tayi waje da gudu duk da bata ganin koda gabanta tsabar duhu. Shi kuwa yana cikin bukkar ya fadi kasa yanata birgima tsabar azaba... Sassarfa kawai takeyi hannuwanta a gaba kamar makauniya. Babu abinda jikinta keyi sai rawa, zuciyarta kuma kamar zata fashe. Gani takeyi kamar ta aikata wani babban lefi, anya Allah zai yafe mata kuwa, to idan ya mutu fa? Haka take tafe tana saƙe-saƙe a zuciyarta. Tayi tafiya mai nisa sosai amma tsabar tashin hankalin datake ciki besa ta saniba. Haske ta fara hangowa a ɗan gaba da ita kaɗan, nan take zuciyarta ta bada dummmm gani takeyi ta kuma haduwa da wasu mugayen ne. Rasa inda zatabi tayi, ga shi ko hasken farin wata babu, ji tayi kamar ta koma baya, to amma a bayan ma me zata tarar? Gefen damanta tabi taci gaba da lalube, aikuwa sai ji tayi ta bugu da bishiya, take ta saki yar ƙara. Haske ta akayi da torch light, Bata ganin komai illa hasken da aka dallare mata ido dashi. Yanda fargaba ta kamata ji tayi kamar ta saki fitsari a wando, Jin taku tayi an ƙaraso kusa da ita, sannan aka ɗauke hasken daga idonta Soldier ta gani tsaye yana kare mata kallo "ke kuma wacece, from where? "Don Allah kayi hakuri" cewar Nawaz a daburce "Babu abinda kika min meyasa kike bani hakuri? "Babu komai? " Ke wacece kuma daga ina kike? Hakanan taji zuciyar ta ta yarda da shi "sunana Nawaz ina daya daga cikin wadanda yan garkuwa da mutane suka kama. Kwalalo ido waje yayi "what? Wai kina nufin kin gudo ne? "Eh wani ne a cikinsu ya taimakeni. Bai kuma cewa komai ba sai Ciccibarta da yayi ya ruga da gudu, gurin hasken da Nawaz ta gani dazu nan ya karasa , yana zuwa ya sauketa a kofar wani ⛺ tent, ashe tantinane dayawa a gurin, duk sojojine wadanda gwamnati ta turo dajin bayan video ɗin da ƴan ta'addan suka tura dazu. "Stand here, and don't move an inch. Wani tent ya shiga da sauri, yana shiga ya ƙame sannan ya sara wa wanda yake zaune a ciki. "Aayann any spot? "Daɗa Sara mishi Aayann yayi sannan yace "sir yes a good one, na shiga cikin dajin ina ɗan dube dube sai nahango wani abu kamar mutum yana zuwa, sai kuma naga ya chanza hanya. Saina bi abin a hankali Nasha gabanshi, ashe wata yarinya ce. To dana tambaye ta dai tace wai tana daga cikin wadanda akayi garkuwa dasu. Da sauri ogan ya mike "were is she? "Tana waje sir" Waje suka fita tare, a inda ya barta nan ya ganta tsaye. "Stupid! mace ka bari tsaye a haka? Come-on ka bata kaya tasa tukuna sai mu yi abinda ya dace. Tent ⛺ dinshi ya buɗe ya shiga , be daɗe ba ya fito riƙe da wandon sojoji da t-shirt ɗin sojoji cotton, Miƙa mata yayi sannan yace "kishiga ciki kisa. Amsa tayi ta shiga ciki, cikin yan mintoci ta fito, kayan sunyi mata kyau sosai. Kallonta Aayann yayi sannan ya kauda kai. A gaba ya tasa ta har dakin ogan nasu , itadai Nawaz sai kakkare jikinta takeyi saboda kayan sun kama jikinta. Guri ya nuna mata ta zauna sannan ya Sara wa ogan shima ya samu Guri ya zauna, Cikin kulawa colonel ɗin yace "ƴata ya sunanki? Ahankali tace "sunana Nawaz Muhammad " zaki iya faɗa mana Abinda ya faru tun daga farko sanda suka zo suka tafi daku har zuwa sanda kika gudo daga wurinsu. "Eh zan iya" "To muna sauraren ki, Kuma ƴata inason ki nutsu kinji.. "To "tace sannan ta fara basu labarin abinda ya faru tiryan tiryan, babu abinda ta ɓoye Musu illa ɗan fashin data gamu dashi wanda Yaso ya kwanta da ita ta Chaka mishi wuka. Ajiyar zuciya colonel ɗin yayi " to Aayann kaji abinda tace koh? Gaskiya fitarka tayi kyau, yanzu zan yi waya can barrack a turo mana da 🚁 helicopter da karin colliques saboda da asuba nakeso mu farmakesu. "And kuma ka tafi da daughter na ka samar mata wani abu taci, kuma ka kular min da ita zuwa safiya sai asan yadda za'a yi. "Yes sir" sannan ya mike yayi waje. "Daughter ki bishi he will take good care of you nasan Aayann sosai... Mikewa tayi itama ta bishi, a waje ta ganshi tsaye yana ganinta yayi hanyar tent ⛺ dinshi... Ta daɗe tsaye a bakin kofar tana wasi wasi, anya in shiga kuwa, kada a maimaita abinda ya faru dazu domin ita yanzu maza ma tsoro suke bata. Kamar daga sama ta jiyo Muryar shi "ki shigo mana" Zirif ta shige saboda iya yan mintocin data haɗu dashi tsoronshi takeji sosai.. Irin katifar da ake pumping dinta da iska ya nuna mata, "ki zauna anan, and kuma me zakici in kawo Miki? "Banajin yunwa" Be kula taba ya tashi ya haɗa mata Black tea ya dauko cake a cikin bag pack dinshi ya kawo gabanta ya ajiye. Can nesa da ita ya zauna, "eat, i want to ask you some questions. Kamshin da tea ɗin yakeyi yasa ta dauka ta kai bakinta tayi sipping a hankali. Ta ɗan sha da yawa sannan taji yace " wanda kikace kun tawo tare dashi sun harbeshi a kafaɗa mijin kine? A hankali tace "a'a yayana ne" "And kuma meyasa dazu kika rufe jikinki da bedsheet, ina kayan ki? Jikintane ya hau rawa, tana tunanin yanda za'a yi ta faɗa mishi abinda ya faru. "Calm down Nawaz, kada kiji tsoro faɗa min koma menene? Yanda yayi maganar sai taji ta samu kwarin gwuiwa, a hankali tace " bayan na gudu daga can shine na haɗu da wasu a hanya, kuma ogansu yaso yayi raping ɗina amma shine na gudu. "Good girl, yanzu ki kwanta kinji, zuwa gobe zamuje mu kama su duka mu tafi dasu duk zasu gane kuransu. Sai sannan Nawaz ta kalli fuskar Aayann. Ganinshi tayi mekyau kamar ba soldier ba harda gyaran fuska da gashi, gashi kyakkyawane sosai Ita tasha iya tsawo gareshi sai yanzu taga ashe me faɗi ne jikinshi a murde yake alamar training. Daga mata gira ɗaya yayi "ya akayi" Da sauri ta juya baya ta kwanta ta ƙudundune jikinta da bedsheet ɗin... Murmushi yayi "good night" Ba barci takeyiba amma sai tayi luf harda numfashin ƙarya . Shi kuma Aayaan mikewa yayi ya dauko laptop 💻 a cikin jakarshi ya kunna yanata dube dube To Nawaz da Aayaan asuba ta gari..... *_MATAR RASHEED_*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *EPISODE 25* *NA HAFSAT ALIYU SHUAIBU CHIKAJI*✍️ Hasken Rana ne ya haska cikin tent ɗin da Nawaz ke kwance, kasan cewar tent ɗin light blue ne kuma yana fuskantar gabas, Hakan sai yasa cikin tent ɗin yayi wani irin hasken kamar wutar nepa, Tashi zaune Nawaz tayi tana mutstsike ido alamun farkawa daga barci, waige waige ta fara yi domin ta manta a inda take, Shiru tayi sanda komai ya dawo mata, babu kowa a cikin ɗakin sai dai tana jiyo hayaniya a waje sosai.. Mikewa tayi a hankali ta ɗan bude labulen tent ɗin ta leka waje, daarararammmm gaban Nawaz ya faɗi, dalilin ganin sojojin da tayi bila adad kowa na sharafin gabansa. Ai da sauri ta saki labulen ta koma ta zauna, tunani ta fara "wai haka rayuwa take dama, duniya juyin juyi, yau ta kaika nan gobe ta kaika chan, Allah Sarki ko ina sarfraz? Yana raye koya mutu, kuma nasan duk inda mummy take tananan hankalinta a tashe, ummi nama nasan tana cikin damuwa.. Oooh nama manta da akwai waya a duniya, ƙilama suna ta kiram mu... Hawayene ya ziraro daga idonta, bata samma ya zubo ba saboda gaba daya ruhin ta baya tare da ita, tunaninta yafi tafiya kan mummy SARFRAZ saboda shi kadai gare ta sannan bata bari yayi nesa da ita amma gashi sanadinta hakan ta faru, kuma tasan takira wayoyinsu har ta gaji... Abu taji ana goga mata a fuska, firgigit ta dawo hayyacinta, Aayaan ta gani durkushe a gabanta rike ta very neat hankie yasa a fuskarta yana tsane mata hawaye. Gira ɗaya ya ɗaga mata "why are you crying? Keda tun ɗazu ake jira ki tashi shine kuma zaki tashi da kuka? Wani hawayen ne ya ƙara zubowa daga idonta "bansan wane hali SARFRAZ yake ciki ba....... Ita kanta bata san sanda maganar ta fito daga bakintaba kawai dai taji ta gama faɗa ne. murmushi yayi mata me kyau "look insha Allah Babu abinda zai sameshi kin ji? Saboda tun tuni aka Turo Ambulance ta kwashe waɗanda suka ji ciwo aka kaisu asibiti don abasu taimakon gaggawa, waɗanda suka rasu kuma ankaisu mutuary kafin ƴan uwansu suzo su daukesu. And please ki kwantar da hankalinki everything will be right insha Allah, Yanzu me zakici? And kuma nasan jiya daƙyar idan kinyi sallolinki koh? Mamakine ya kamata "au dama sojoji suna sallah, lallai Allah al Hakeem ne, ai ita tasha faɗa da harbe harbe be barinsu su tuna da sallah, to kuwa indai hakane sun isa a Sara musu.. Nawaz ke zancen zuci Husky voice dinshi ta daɗa ji yace "sister bakice komai ba. " To ameen Allah yasa yana raye, sannan ruwan alwala zaka fara bani inyi sallolin saboda tun sallar azahar ɗin jiya ban kuma yin Sallah ba. "Okay bari nazo" fita waje yayi be daɗe ba ya dawo rike da bottle water Guda biyu. Bata ruwan yayi sannan yace kiyi alwalarki a gefen nan kawai basai kin fita ba, akwai maza da yawa a waje. Idan kuma za kiyi easing kanki ne to sai in raka gurin da zaifi _safe_. Da sauri tace "A'a banaji Nagode, be kuma cewa komai ba ya juya ya fita daga ɗakin.... Gefe ta samu tayi alwalar sannan kuma ta koma ta zauna tana tunanin dame zata rufe jikinta tayi sallah, dai dai nan Aayaan ya dawo, Be kula taba ya wuce ya bude wata luggage 🧳 me jikin sojoji ya ciro wani farin plain din zanin gado, hannunshi yasa ya yaga shi biyu, ajiye ɗayan yayi a gefe sannan ya miƙa mata dayan, "Ki rufe jikinki da wannan sai kiyi sallar, Amsa tayi "Nagode" Fita ya kuma yi, tashi tayi ta fara jero sallolin da ake Binta haɗe da yin addu'ar samun sauki da rangwame agurin Ubangiji Allah, Ta kusa idarwa Aayaan ya shigo riƙe da bowl guda biyu, A gefenta ya ajiye shima ya zauna, Bayan ta idar ta kalleshi a sanyaye tace "ina kwana" Murmushi yayi "lafiya lau, ya fargaba? Allah ya tsare gaba kuma yasa dan uwanki yana raye... "Ameen, Nagode Allah ya saka da Alkhairi, kulawar da taimakon da kamini. Murmushi ya kuma yi "kada ki damu Saida na rantse akan zan taimaki kasata kafin nan na zama cikakken soja, kuma aimu dama bayin kune masu kula daku.... Zaro ido Nawaz tayi "wai!!! nifa Wallahi bance hakaba. Murmushi yayi bece komaiba, bowl ɗin ya tura mata gabanta "idan kika gama ci colonel yana kira" sannan ya tashi ya fita. Cikin bowls ɗin tabi da kallo, bowl ɗin farko farfesun naman kaji ne sai na biyu wani abu kamar koko kamar Golden morn gashi nan dai, cokalin dake ciki ta dauka takai bakinta. Jin ɗanɗanon tayi kamar ansawa kunun alkama madara, kaɗan tasha ta matsar dashi gefe, shima farfesun bata wani sha da yawa ba. Zanin da tayi sallah ta dauka ta rufe kanta dashi sannan ta miƙe tayi hanyar fita, a hankali ta buɗe labulen ta fita.. Sojoji ta gani bila adad wannan yayi chan wannan yayi nan, wasu kuma na gefe suna duba bindigogi wasu kuma suna wajen motoci irin na yaƙi Aɗan gaba ta hango wasu a gaban manyan tukwane, " oh wai dama mazane suka dafa abincin, hu'umm sojoji na ƙoƙari... Duk ta hargitse ta rasa inane tent ɗin colonel ɗin, ɗan gaba tayi kaɗan sannan ta fara waige waige, kallonta sojojin suka farayi suna mamaki "wannan daga ina kuma! Kayan sojojin is familiar to them kuma gata karama, su sam basu taɓa ganin taba ma.. Wani ne ya nuno ta da bindiga "hey you, from where? Fitsari ne taji yana kokarin zubowa , jikinta sai rawa yakeyi. Batasan sanda ta ɗaga hannuwanta sama ba ta rufe ido, itafa yanzu gaba ɗaya jinta take kamar ba ita ba Duniyar ma ta isheta. Muryar Aayaan taji yana cewa "kai mara hankalin inane? Macen kake nunawa bindiga? Me aka fara faɗa mana kafin mu fara aiki? Natsuwa kowa yayi, hakan ya nuna yanada wani babban matsayi, shikuma da sauri yace "I'm sorry sir, wallahi wasa nakeyi mata, naga ta fito ne tana raba ido kamar tanajin tsoro "Okay shine kake so ka daɗa razanata koh? To da ta faɗi fa? Kuma kar kaga kamar nabar maganar i will get back to you. Gurin Nawaz ya ƙarasa wadda har yanzu idon ta na rufe, "Open your eyes" ya fada cikin soft and husky voice dinshi.. ke kin cika tsoro Wallahi.... A hankali Nawaz ta buɗe idon ta amma har yanzu jikinta rawa yake kamar ace kyak ta ruga da gudu... Gaba ya shiga tabi bayan shi da sauri har ɗakin colonel ɗin... Bayan sun zauna ne colonel ɗin ya kalleta cikin kulawa yace "my daughter how was ur night? "It was...... Kasa ƙarasawa tayi sai kuma ta kalli Aayaan. Murmushi colonel yayi "yea u are right Aayaan ya kamata na tambaya ya kika kwana ba ke ba. Smirking kawai Aayaan yayi amma bai ce komai ba, "Yauwa daughter kina ganin daga nan zuwa gurin da ƴan ta'addan suke zai Kai kilometer nawa? "Ehm gaskiya da nisa kuma bazan iya tantance kilometers nawa bane, amma dai tun magrib na gudo sannan kuma gudu nayi .. "Sir and kuma ni na ganta ne misalin 2:28am kaga ta kwashi kusan 7hours kenan tana tafiya.. cewar Aayaan "Yea u are right, Amma banji daɗi da ba'a Turo mana da 🚁 helicopter dinba, naso ace zuwa yanzu mungama abinda zamuyi saboda kowa a shirye yake. "Sir kada ka damu insha Allah ko wane jinkiri za'a yi mu zamuyi nasara. Cewar Aayaan yana kallon colonel ɗin Ita dai Nawaz mamakin yanda Aayaan ya shaku da colonel takeyi, kuma duk tanajin abinda suke cewa cikin fahimta. Colonel ɗin ne ya kalleta "daughter Dake zamuje kema kiga yadda za'a yi musu koh? Zaro ido tayi waje kuma ta kasa furta koda kalma guda ɗaya..... Dariyar ciki Aayaan yayi yana kallon ta, " sir ai wannan matsoraciya ce, yanzun nan ma na tarar Daniel ya nuna mata bindiga bakaga yadda jikinta ke rawa ba.... "Stupid wai ku meyasa bakusan darajar mata bane, kuna mantawa ko yaƙi zamuje garin maƙiya ana faɗa mana cewa kada mu taɓa mata da yara... Kuma ko ba haka ba an fada muku cewa ku zaku iya yin Abin da Mata keyi ne? Duk ƙarfin nan da kuke takama dashi to itafa ta haifeku kuma da bata kula da kuba kun isa ma ku rayu balle har ku zama wani abin, Amma ku yanzu kun maida mata abin tsokana koh? " I'm sorry sir" Aayaan ya fada cikin girmamawa. Ita kuwa Nawaz sakin baki tayi tana kallon colonel "wai wane irin muhimmanci sojoji sukeba mata ne, itafa abin mamaki yake bata, ashe shiyasa Aayaan yaketa hidima da ita.... Kallon Aayaan tayi, ɗaga mata gira yayi alamun ya akayi? Ita dai idan ya ɗaga girar har mamaki yake bata amma yanzu ta ajiye cewa ɗabi'ar shice ya riga ya saba... Kauda kanta tayi gefe... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Mummyn sarfraz ce zaune taci uban kuka har ta godewa Allah, domin tun a jiya labarin ƴan ta'addan ya isa gurinta tunda gaba daya anyaɗashi a labarai da internet... Gashi kuma ta kira wayar SARFRAZ harta gaji, da idan ta kira tana shiga dauka ne kawai ba'a yi, amma yanzu idan ta kira sai dai taji ana cewa switch off... Daddy ne ya kalleta "ɗan Allah Madam kiyi hakuri ki Dena kukan nan, Wallahi Nima zuciyata a karye take kawai dai ina boyewa ne saboda kada abin yayi Miki yawa. Share majina tayi "haba maigida yanzu ace ga abinda ya faru kuma sai na zauna, yaron nan shi kadai fa Allah ya bamu yanzu ace ya mutu shikenan mu bamuda Magaji kenan kuma bamuda meyi mana addu'a, da acema yayi aure ne to nasan matar ta haihu koma bata haihuba kila tanada ciki. Amma yanzu babu ko ɗaya, ƙara fashewa tayi ta wani irin kuka mai cin rai, wayyooo Allah na, na shiga uku Allah ka duba halin da nake ciki kada ka rabamu da SARFRAZ, Shidai dady sai ya zama ɗan kallo don ya rasa ma yanda zai yi mata, gashi shima zuciyarshi sai ƙuna takeyi mishi daurewa kawai yakeyi... Ganin mummy yayi ta mike zumbur "wallahi can zani Gara naje na duba idan yana raye inma baya raye Gara ko gawar shi na gani, nasan idan na zauna bakin ciki ne zai kasheni. Shima mikewa yayi yabi bayanta cikin sauri.. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ummin Nawaz ce zaune ta tafka uban tagumi, ƙuna kawai takeji a zuciyar ta, sam ta rasa me keyi mata daɗi a duniya, Baffa ne yace "duk abinda ya faru Ni naja tunda Ni na matsa akan sai tazo garin nan, nadan da bance ba da babu abinda zai faru amma yanzu sai Allah saboda kuna gama waya da ita aka fara sanarwar yan ta'addan sun kwashe mutane "A'a baba ba laifinka bane haka Allah ya riga ya tsara, koda baka ce tazoba sai hakan ta faru. Amma ce tace "Ni wallahi jiran tsammanin nan ya isheni Saboda duk minti ɗaya zuciyata ƙara tsinkewa takeyi, wallahi dama mun bishi can mutuary ɗin... Jugum jugum sukayi kowa da abinda yake saƙawa a zuciyarshi..... Yau dai bamu leka gurin SARFRAZ ba..... _*MATAR RASHEED*_*🎀🎀SARFRAZ*🎀🎀 *Episode 26* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji* Koda gari ya waye haka bandi ya Daɗa haɗa magungunan yaba sarfraz, sannan ya tatso nonon ya kuma ɗura mai.. Ita dai hassu sai dai tayita kallonshi, yana burgeta dukda baya ko motsi, ga wani uban tausayinshi da takeji. Tasan wahalar da baban kawarta yasha da duk wani iyalinshi lokacin da paralyze ya kamashi.... Shi yasa take jinjina ta yadda zasu kula da wannan bawan Allah. Gashi iyayensu sun tafi gabas kiwo da neman magunguna, kuma basa dawowa Sai sun shekara wani zubin ma suna wuce shekara. Kasancewar su dama tun usuli fulanin dajine waɗanda akasarin su basa zama a guri ɗaya.... Kuma mahaifinsu ya kasance likitan gargajiya. Ita dama tun tasowarta bata wani saba da iyayenta ba sosai kasancewar basa zama, tafi sabawa da bandi saboda kullum suna Tare kuma yana kula da ita sosai domin duk abinda takeso shi yake yi mata, kuma sam bayason abinda zai tayar mata da hankali ko kaɗan .. Kallonta ta maida kan bandi tace "bandi kana ganin zataji sauki har ta tashi? "Hassu ka kwantar da hankalinka zataji sauki kuma zata tashi insha Allah.. Zanta kulawa da ita har sai su baba sun dawo sai yayi mata magani. Koda lokacin tafiya kiwo yayi sai bandi yacewa hassu ta zauna ta kula da sarfraz, shi zaije saiya dawo... Rakashi hanya tayi sannan ta dawo ta zuba wa Sarfraz ido tana aikin nata wato tunani.... Sai dai lokaci bayan lokaci tana zuwa duba shi... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ba'a daɗe ba taji iska na kaɗa tent ɗin da suke ciki ga wata kara mai ƙarfi. Murmushi colonel yayi wa Aayaan "i guess sun iso" "Yes sir insha Allah" Aayaan yace yana miƙewa, shima colonel mikewa yayi suka yi hanyar fita. Ganin Nawaz batada niyyar binsu yasa colonel tsayawa "daughter taso muje mana" Miƙewa tayi a sanyaye tabi bayansu, ile kuwa helicopter ne guda hudu duk fentin jikinsu kalar uniform ɗin sojoji, farfelar su nata juyawa kura na tashi. Gani tayi colonel yayi gurin jirgin, shima Aayaan nan yabi, ai saita tsaya tana rarraba Idanuwa, ita gaskiya ko jirgin arziki bata taɓa hawa ba bare wannan wanda ko ƙofa bashi da ita... Har sun shiga colonel ya waigo sai ganin Nawaz yayi can nesa a tsaye "Aayaan kalli daughter bata biyomuna ashe" Ai cikin kwarewa Aayaan ya diro daga cikin jirgin da hanzari ya nufo inda take cikin taku ƙalilan ya iso gaban Nawaz kafin tayi wani yunkuri ya sunkuceta ya juya zuwa jirgin, Saida ya saka ta sannan shima ya shiga. Tsaki Nawaz keta ja, azuciyar ta "nidai naga ta kaina daga wannan sai wancan, toni haka rayuwata zata ƙare ne, daga hannun wannan namijin sai hannun wancan, Allah gani gare ka... Jin Muryar colonel tayi yana cewa"daughter kin manta nace Dake zamuje shine zaki tsaya a baya? Firfito da idonta tayi waje " sir please I can't stay in here" wallahi tsoro nakeji "Babu abinda zai sameki, ki kwantar da hankalinki, abinda yasa nakeso ki bimu shine don kiga yanda za'a firgita ƴan ta'addan Da suka firgita ki, Tana tsakiya, colonel yana gefen dama Aayaan yana gefen hagu, shi dai duk hirar da akeyi yana jinsu iyakacinsa yayi murmushi, dama shi koba yanzu ba miskilancinshi yafi maganar shi yawa... "Kamar ta zunduma ihu sanda jirgin zai tashi sama duk tabi ta daddafe seat din da driver yake kai kamar zata fincikoshi.... Idonta a rufe yake tanajin kamar zata faɗo kasa daga cikin jirgin, a cikin zuciyarta take ayyanawa "dama ace tun sanda ummina tayi tafiya duk abinda ke faruwa mafarkine ba gaskeba... Amma ina tasan gaskiya ne babu yadda ta iya face ta amshi kaddara.... Dayake a cikin jirgi ne ƴan mintoci ƙadan taji ana cewa "mission x is detected" Ita dai tadaiji maganar ne amma batasan ta inda take fitowa ba. A hankali jirgin ya karkace gefen dama zaiyi corner ai ƙara Nawaz ta saki ta riƙunƙume Aayaan da karfi... Be kalletaba be hantaba, shidai still Yana nan inda yake ko motsi beyiba .. Yan mintoci ƙadan aka wuce gurin sai kuma a hankali a hankali jirgin yayi ƙasa.. Saida Nawaz taji kamar an tsaya sannan ta buɗe ido a hankali, ajiyar zuciya ta saki ganin da gaske an tsaya, sai sannan ta saki rigar Aayaan cikin jin kunya, beko kalleta ba ya gyara rigar shi ya dira daga jirgin . Hannu ya miƙo mata alamun tazo ya sauketa babu musu ta mika mishi, kamar ƴar tsana haka ya direba a waje... Duka jiragen ta gani sun sauka duk sojoji ne birjik kowa da shigar yaƙi.. Colonel wanda sai yanzu ya fito ya kalli Aayaan "Aayaan ka samata bullet proof vest saboda banaso a samu wata matsala... Cikin dajin suka shiga suna sanɗa, basu ankara ba saikin karar bindiga sukayi a gabansu bullet ne ya fito yayi santar kan Nawaz ai cikin hanzari Aayaan yasa hannu yayi ƙasa da ita bullet ɗin ya chaki tafin hannunshi.. Ai babu shiri colonel ya Basu order harbi, tuni sukayi cikin dajin suna harbi ta ko ina, sai babbar bindigar dake hannun wani soja tun dazu yana kusa da colonel yana jiran order , yatsa kawai colonel ya hada take wannan sojan ya saki kunamar bindigar ,wani abune kamar bullet amma babba yayi cikin dajin da gudu ji kake bummmm ya fadi a kasa .. Duka sojojin ne sukayo baya, ganin an saki fainting gas din, don ma suna sanye da hular sojoji da sai abin yayi affecting Dinsu. Gaba ɗaya jikin Nawaz sai rawa yake yi yau itace aka saito da harsashi lallai Allah yana sonta dafa yanzu sayu buzun ta, shi ko Aayaan ko a jikinshi kamar bashi aka harba ba, bakinshi yasa a daidai inda bullet ɗin ya cakeshi yi ya finciko bullet ɗin ya yar a gefe sannan ya yagi gefen rigar shi ya nannande gurin. Sai sannu Nawaz takeyi mishi, ga uban tausayinshi daya kama ta, a dalilinta haka ta faru, colonel ne ya karasa inda suke "Aayaan you've really try, good job, i have an unexpected gift for u bayan mun koma barrack. Sannu hope is not that much painful? Murmushi Aayaan yayi "sir u taught us how to ignore pain, Murmushin shima colonel ɗin yayi "is that really working? "Not really" cewar Aayaan Yana kallon Nawaz dake duƙe akan gwuiwotinta a gabansa... "Tashi, don't worry I will be fine, just take care Sai da aka ɗauki kusan minti goma sannan suka kutsa kai cikin dajin, mutanene kwance ta ko ina birjik babu wanda yake motsi Da gudu Nawaz ta karasa kusa da mai cikin nan ta tsuguna tana taɓata, "shikenan yanzu duk kun kashesu, wallahi banda su iya waɗan can ne ƴan ta'addan, amma banda waɗannan.... Meyasa zaku kashe kowa? Ba cewa kukayi Zaku ceto suba. "Ooooohhhhhh talkative, wai meyasa ke bakya iya ganin abu kiyi shiru ne? Aayaan yace cikin ƙosawa da maganganun ta. Colonel ne yace "No Aayaan, meye amfanin kasan abu kuma kaƙi sanar da wani, ai kamata yayi kayi mata bayani yanda zata gane. "Yes sir" cewar Aayaan yana Sara mishi, sannan ya kalli Nawaz "ba mutuwa suka yiba barci sukayi me kamar suma sai bayan awa ɗaya duka zasu farka. Wani gas ake jefawa idan ya fashe to duk wanda ke gurin saiya suma amma banda wanda yasa mask, amfanin shi shine idan aka jefa za'a banbance yan ta'addan da innocent ɗin sai a kwashe su duka a kaisu asibiti su kuma yan ta'addan asa musu hand curve sannan a kwashe su duka a mikasu federal C I D. Girgiza kai tayi alamun gamsuwa, sannan ta farabi tana nuna musu yan ta'addan ana sa musu hand curve sannan wasu sojojin suma suna ɗiban makaman su suna zubawa a cikin jirgi, wasu kuma sai ɗiban wadanda akayi kidnaping ɗin suke suna zubasu a wani jirgin daban, karasowa sukayi gurin iluu kallonshi tayi tai shiru sai tace Banda wannan shima satoshi akayi, basu Musa mataba kasancewar bai rufe fuskarshi da rawani ba, kuma babu bindiga a hannunshi. Tsaff aka gama sawa yan ta'addan hand curve, sannan an gama kwashe mutanen da makaman, Kunna jirgin sukayi don kai mutanen asibiti sai kuma ɗaya jirgin wanda aka zuba makamai shi kuma Abuja zai wuce... Suma yan ta'addan aka loda a ɗaya jirgin don a wuce Abuja dasu suma,. Babu gurin dasu colonel zasu zauna sai suka zauna a gefe kafin jirgin da zaije general hospital ya dawo... Kallon Aayaan Nawaz tayi "sannu, kanajin zafi koh? Kuma Ni naja maka, I'm sorry, Dariya abin keba Aayaan yanda ta wani damu '' nace calm down babu zafi and I'm use to it, Sannan nake bace... Colonel dai yana gefe yana kallonsu yana ayyana wani abu a zuciyarshi... A hankali Nawaz tace yauwa "su sauran ba anan sukeba suna gaba, "To ai waɗannan tuni na gama da babinsu tun kafin ki tashi daga barci, nasa anje an kwaso su su bakwai ne yan fashi ne, sai kuma yayi ƙasa da muryarshi "Ashe kisa kikaso kiyi jiyan? Kuma inaso Nima a koyamin yanda ake sarrafa wuka.... Kunyace ta kama Nawaz ta mike tayi gaba da sauri. Ba'a ɗauki lokaciba jirgin ya dawo ya kwashe su, asibiti ya fara kaisu Nawaz ta tarar duk waɗanda aka sace su tare sun farfaɗo wasu ana ƙara musu ruwa wasu an kawo musu abinci, anan aka faɗa mata mai cikin nan tana labour room. Iluu ta hango, da sauri ta karasa kusa dashi "ilu ya jiki? Godiya zai fara yi mata tayi kasa da murya tace kada ka gode min kaikayi sanadin da kowa ya kubuta, don Allah ka tuba kadena wannan abin kaji, kasan dai sauran basusan fuskarkaba to ka samu ka ƙoƙarta ta tafi gida kafin wani abun ya kuma faruwa... Colonel ne ya kirata suzo su tafi an gama yiwa Aayaan dressing ɗin ciwon. Nawaz ce tace "inaso naje gida! " Zakije amma sai kin samu nutsuwa yanzu kibi Aayaan zai dauki information ɗinki sai a kira can gidanku a faɗa musu kina lafiya daga nan kuma sai a kaiki gida kafin governor ya nemeki don abaki award... Taɓe baki tayi, irin su award manya ita award be dametaba sarfraz takeson gani, Ai da sauri tace a ina aka kawo mutanen jiya wadanda ƴan ta'addan suka harba.. Wani ward aka nuna mata, tas ta zagaye gurin bataga sarfraz ba, zuciyarta ce ta tsinke innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, shikenan sarfraz ya mutu kome? Ai ihu ta fara rafkawa take idon kowa ya dawo kanta, ganin ta sanye da kaya sojoji kuma tana tafka uban ihu, colonel ne yace menene? "Banga yayana ba shikenan ya mutu, don Allah ku kaini mutuary inga gawarshi. Colonel ne yasa aka rakashi mutuary ɗin amma abin mamaki nanma babu sarfraz baby alamun shi . Damuwace ta kama Nawaz ne ƙarfi "ina sarfraz yake, me ya sameshi? Tafe suke hawaye ya na zuba a fuskarta, Bakin asibitin suka fito, motocine guda biyu sukayi parking a gabansu, colonel ne ya shiga daya yana musu sallama "saimun haɗu a Abuja , and please take good care of your self and my daughter... Ayaann ne ya shiga daya motar itama tabi bayan shi ta shiga... Duk wani iri takejinta, kewar gida ta kamata ga damuwar ina sarfraz yake,,, Tana ta tunani ta saƙa wanna ta warware ta saƙa wancan shima ta warware,. A haka barci yayi awon gaba da ita (mayyar bacci mota) Ji tayi ana yi mata tafi a fuska, firgigit ta buɗe ido "ki fito mun gida" A hankali ta sauko tana bin gidan da kallo "Allah mai halitta, lallai duniya dama ance a Fika ne kaima kafin wani, duk irin kyan da take gani na gidansu SARFRAZ sai taga wannan ya damashi ya shanye... Babu abinda babu a cikin gidan dangin su swimming pool, garden, gym, football field hand Ball field, parking space, meeting point, sai can wani guri data hango runfunan bunu masu kyau ga dawisu sai yawo suke a gurin can gefe kuma harda su jimina.... Bin bayan shi tayi ganin yabi wata hanya, a bakin wata haɗaddiyar kofa taga ya tsaya, a cikin wani sensor ya saka yatsanshi babba. Take kofar tayi sliding, yana shiga itama tabi baya shi da gudu ta shiga, ai kusan suma tayi ganin cikin ɗakin. Gaba daya komai design ɗin Larabawa ne zaka iya rantse wa ba'a Nigeria kake ba, tsayawa ma siffanta falourn kamar rage mishi kyau ne, Duk ta tsargu sai take ganin anya batayi azarɓaɓi ba, dama bata shigo ba. Ɗan gefe taja ta tsaya tana rarraba Idanuwa, wata mata ce haɗaddiya mai cike da haiba da kwarjini a shekaru bazata fi hamsin zuwa hamsin da biyu ba ta fito daga wata kofa, ai da gudu ta tawo shima Aayaan ganinta yasa ya nufeta da gudu, yana zuwa ya ɗagata sama "my world nayi kewar ki sosai" sannan ya sauketa ya rungume ta, Nan ya fara yi mata shagwaɓa kamar ƙaramin yaro, ita kuma tana biye mishi Ɗagowar da zatayi kawai tayi ido huɗu da Nawaz wadda ta saki baki da hanci tana kallon yanda Aayaan yake abu kamar ƙaramin yaro, kamar ba soja ba.. Murmushi tayi "wacece wannan" tace cikin Yaren Larabci... Nan Aayaan ya kwashe komai ya faɗa mata shima da harshen larabci... Nawaz na gefe tanajin duk abinda suke faɗa, Hancinshi taja "har Nasha ko nayi suruka ne, naganta kyakkyawar gaske, Gaban Nawaz ne ya bada dumm, shima ɓangaren Aayaan hakane ta faru sai ya dago ya kalleta a hankali.... Gun Nawaz amma ta ƙarasa ta rungume ta haka kawai ita taji yarinyar ta birgeta kuma ta natsu da ita sosai, tunda amma tayi maganar cewa Nawaz ko surukar tace kirjin Aayann keta bugawa da karfi .... _*~MATAR RASHEED~*_✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀🎀* *Episode 27* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Yanda ya fita ya bar su haka ya dawo ya samesu a inda suke, baffa ya kalla "baffa babu inda ba'a kaini ba, tun daga kan dakin majinyatan har dakin waɗanda aka kwaso har mutuary babu Nawaz sam.. Fashewa da kuka baffa yayi "shikenan abinda nake fargaban ji Saida naji shi, yanzu shikenan ba'a ga nawwaraba? Nura ne yace "baffa kayi hakuri insha Allah za'a ganta tunda ai bata cikin gawarwakin. Amma ce tace "Nura kayi shiru kawai, kaifa yanzu da bakinka kake faɗa mana har asibitin kunje amma bata, to a ina za'a ganta kenan? Ummin Nawaz tace "baffa da amma kuyi hakuri kawai mu dauki kaddara haka Allah ya tsara, amma mu zauna muna daɗa ɓata wa kanmu rai bashida wani alfanu... Ni nayi imani da Allah kuma nasan komai ya faru haka Allah ya tsara tun farko... "Yanzu ke da zamuba hakuri mu kike ba? Allah yayi Miki albarka kuma insha Allah sai hakan ya zame mana Alkhairi dukan mu.. Nura dake gefe yace "Amin" yana goge hawaye.. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Mota mummy zata shiga dadyn sarfraz Yace a'a bazaki iya driving ba, Nima da nake na miji bazan iyaba, yanzu abinda za'a yi shine Ni zan tuka motar muje tasha Achan saimu samu driver ya kaimu ya dawo damu inyaso sai ya fadi nawa zamu bashi, Haka kuwa akayi suka samu driver akan shi zai kaisu ya dawo dasu amma a motar su, sannan suka dauki hanya... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° A hankali ta saki Nawaz daga rungumar da tayi mata "ƴata ya sunanki? Amma ta faɗa cikin Hausar ta mara fita.. "Sunana Nawaz" cewar Nawaz a hankali... "Wow sunanki is special, kada na dameki zo muje in rakaki ɗakin ki ki samu kiyi wanka kici abinci kiyi barci ki huta idan kika tashi sai muje gidanku mu kaiki ko? "To" Nawaz tace tana mamakin wai takaini ɗaki na, to a ina ya zama nawa? Bakin wata ƙofa ta tsaya tayi danne danne sannan ta kama hannu Nawaz tasa a cikin sensor ɗin dake jikin kofar take kofar ta buɗe, Sakin baki Nawaz tayi, murmushi Amma tayi mata "it is your room, kije ki shirya, hannunta taja ta saka a cikin ɗakin sannan ta rufe mata kofar ta koma gurin Aayaan... Ganinshi tayi ya cika yayi famm, dama tasan za'a rina Domin Aayaan akwai baƙin kishi.. Ƙarasawa kusa dashi tayi "sweet heart Yana ganka haka? Ko kanajin zazzaɓi ne? Pls kaje kasha magani kayi wanka kaci abinci saika kwanta kafin a kira sallah ko? Shagwaɓe fuska yayi "mummy wallahi kinsan abinda ke damuna shine kika chanza magana! Oh oh oh! Aayaaaann Wai har yanzu baza'a Dena kishin nan ba? Yanzu fa ka girma. Mikewa yayi "shikenan ai dama na lura kina ganinta kika manta dani, Saida kika gama shirya ta sannan kika dawo gurina. Kawai don Allah yayi ni namiji ke kuma mace kikeso shine za'a riƙa nunamin wariya.. Da sauri ta rufe mishi baki "I'm sorry, ba haka bane, she is our guest, ya kamata muyi comforting ɗin ta, amma daka shigo saika kyaleta a tsaye bakace ta zauna ba baka bata ruwa ba, and kasan wannan ba halin musulmi na kwarai bane... Kuma Ni na kula tane saboda na wanke laifin da kayi Murmushi yay "to mum Amma kada ki kuma kyaleni kinji? "To" kawai tace tana mamakin halin Aayaan da bazai chanzaba... Dtaga hannu Aayaan yayi sai sannan amma taga bandejin dake hannunshi Hankalin tane ya tashi ta rike hannun "Aayaan me ya sameka a hannu? Murmushi Aayaan yayi "mum kada ki damu pls na bigene shine na ɗan ji ciwo. Kallon shi mum tayi "haba Aayaan nasanka sarai ba bigewa kayiba ka fadamin gaskiya Murmushin ya dada yi "mum gaskiya na faɗa Miki, please ki bar maganar.. Addu'oi tayi mishi tana Dada sa mishi Albarka, Shima ɗakin dake gefen wanda Nawaz ta shiga yasa hannu a sensor ɗin ya bude sannan ya shiga. Direct bathroom ya shiga yayi freshing up sannan ya fito, ko mai be shafa ba yasa farar armless ɗin riga da three quarter din wandon sojoji.... Ya mike da niyyar fita dining ya ci abinci, sai kuma ya koma ya zauna. Laptop ya dauka yayi danne danne saiga Nawaz ta cikin Laptop din zauna akan gado ta tafka uban tagumi tanata zubda hawaye... Tsaki yayi "shit wai kukan na meye ne? Tashi yayi ya fita falour gurin mummy, zama yayi a kasa ya dora kanshi a cinyarta .. "Mummy Nawaz Bata fitoba kije ki duba ta saiki zo muci abinci... "Okay dear bari nayi checking dinta i am coming .. Tana mikewa ya fito da wayarshi a aljihu yayi dialling ɗin number colonel. Mamakine ya kama mummy ganin nawaz zaune tana shirga uban kuka, da sauri ta karasa gurinta ta dafa kafaɗarta "daughter meya faru? Ko Bakya son gidanmu ne? Girgiza kai Nawaz tayi, "To menene" Cikin Muryar kuka Nawaz tace "ba'a ga sarfraz ba kuma inaso naga mummy da ummi na.. "Okay calm down my dear, kije kiyi wanka, akwai kaya acikin closet saiki zaɓi wanda yayi Miki ki shirya kizo falour muci abinci saimu tafi.. Goge hawayen Nawaz tayi "to amma Nagode" sannan ta mike sai kuma ta waigo "amma bansan bathroom ɗin ba, wata kofa ta nuna mata Sannan tace kisa babban tumb dinki zata buɗe saikiyi Wankan.. Komawa falour tayi dai dai lokacin da Aayaan ya gama waya da colonel Cewa yayi "amma colonel yace wai governor yace yanaso yaga Nawaz and yan majalisa da yawa ma suna so suyi mata kyauta, wai ashe Akwai yan uwansu da yawa daga ciki harda babban yaron ministan kudi, da matar ministan ilimi. Murmushin mum tayi "ai shiyasa nace maka yarinyar tawa ta musamman ce mijinta ma sai nayi mishi screening tukuna, idan yaci sai a daura auren. Kallon ta yayi "mum wai yaushe ta zama ƴar takine? Kuma Ni basai kinyi min haka ba zansan kin Dena kauna ta ba. "Oh oh oh Aayaan wai yaushe zaka dena wannan kishin naka ne, kaifa ba yaro bane yanzu? "Kuma inada tabbacin yanda Nawaz take da kirki nasan iyayenta ma haka suke, zasu bani ita . "To mum Allah ya taimaka Ni nayi nan, hanyar dining yabi. Serving din kanshi yayi sanan ya fara ci beko kuma kallon inda mum take ba. Mamaki abin yaba mum "wai meyasa Aayaan bazaisan ya girma bane? Itama kyaleshi tayi bata kuma cemishi komai ba.. Ita dai Nawaz tana bayi tana wanka, koda ta fito tsayawa tayi gaban dressing mirror, lotion ta shafa sai light blonde powder data shafa kaɗan a fuskarta, tadansa wet lips me kyalli da bakin kwalli a idonta. Ita kanta Sai taga tayi wa kanta kyau... Ga idonta yayi wani haske madaidaicin lebenta yayi kyau kamar tasa light pink ɗin lipstick me ƙyalli. Ta daɗe a gaban closet ɗin, shahada tayi ya buɗe. Wow abin gwanin ban sha'awa, gefen komai daban, laces, Atampa, Materials, Shadda, Hijabs, wandina da tops masu kyau, Abaya, lafaya, Shoes, komai dai gasuna . Idonta ne ya faɗa kan wata abaya ja anyi mata aiki a hannu da kirji da bayanta, Sannan anbi jikin aikin da Stones... Cireta tayi a jikin hanger ɗin tana addu'ar Allah yasa tayi mata dai dai. Pant ta zaba da bra masu kyau tasa sannan ta saka abayar, Saida tayi tsallen murna ganin rigar tayi mata daidai kamar an gwadata... Gaban mirror ta koma tana kallon kanta tana murmushi, sai sannan taga dan ƙaramin akwatin dan kunnaye, budewa tayi suma da yawa, nan dai ta zabi wani fashion Golden colour me baza. Taje kanta tayi ta maida ribbon dinta... Sannan tayi rolling din gyalen, kasan cewar yadin rigar irin mirror ɗin nanne sai tabi jikinta ta fidda shape dinta mekyau musamman kirjinta sai kuma wajen hips dinta da ya buɗe kamar faranti. Har zata fita sai ta tuna ya kamata tasa takalmi, closet din ta buɗe, da kyar ta samu wani flat Golden colour me stones tasa sannan tayi hanyar fita. Dai dai nan Aayaan ya gama cin abincin shi ya mike, mum bari na shiga na kwanta, "Stop Aayaan kada ka kwanta Please inaso akai Nawaz gida yanzu saboda hankalin ta ya kwanta suma ƴan gidan nasu ya kwanta susan tana raye. Inyaso sai mu rokesu mu dawo da ita sai ku tafi Abujan koh? "To" kawai yace ya shige daki domin shi yanzu mum ma mamaki take bashi... Yana shiga Nawaz na fitowa, tsaye mummy tayi tana kare mata kallon "tabarakallahu ahsanal kaliƙin, ashe kwatakwata da bataga kamaiba a kyaun Nawaz. Lallai kam bazata bari Wannan kyakkyawar hajar ta wuce ɗanta ba, duk da ta lura shi ɗin ɗan tijarane... Tarbo ta tayi "Masha Allah, Masha Allah, yarinyata kinga kyaun da kikayi kuwa, gaskiya kinyi kyau... Ki zauna kici abinci kafin Aayaan yayi wanka saimu tafi koh? Murmushi Nawaz tayi "To Amma Nagode Allah ya saka da Alkhairi... "No no my dear kidena gode min, kefa ƴa tace ko Bakya sona a matsayin mama? "Ina so sosai, Nawaz tace cikin jin kunya. Yauwa kokefa yanzu muje kici abinci n, mikewa sukayi suka ƙarasa dinning, da kanta tayi serving din Nawaz , taɗan ci da yawa sannan tasha green tea ɗin da Amma ta miƙo mata.... Falour suka koma suka zauna, waya mummy ta miƙa mata "gashi kiyi game kafin na fito saboda kada ki gaji da jira, zanje na shirya. "To Nagode" Nawaz sai jinjina irin kulawar amma takeyi, sai kuma ta tuna da mummyn sarfraz, Allah sarki ko tana wane hali oho? Buɗe wayar tayi tana ɗan dubawa, cikin Sa'a kuwa taga make up game , ai take ta shafa ta fara yi tanata murmushi... Fitowar Aayaan kenan daga ɗaki zai fara ƙorafi, kawai ya hango ta, Tsaya wa yayi sosai yana so ya gane wacece, a iya tunaninshi ya kasa tuna inda ya santa gashi fuskarta is familiar to amma bari mum ta fito ... Gaban fridge ya karasa ya dau ruwa yana sipping a hankali.. sai kallonta yake yanaso ya tuna inda ya santa, yama manta da batun wata Nawaz . Mum ce ta fito sanye da baƙin lafaya me ratsin ja, "Au ashema ka fito inata sauri inzo in kiraki? Murmushi yayi "na fito mum, amma mum baƙuwa mukayi ne? Kallon mamaki mum tayi mishi kana nufin baka gane daughter na ba, Aayaan banason wulaƙanci fa? Ruwan dayake shirin haɗiyewa ne yabi ta ƙaramin maƙoshi, ai take ya kware ya fara tari Nawaz da hankalinta nakan game dinta, sai jin tari tayi, ai da gudu ta mike tare suka ƙarasa gabanshi ita da mummy, Sannu kawai suke mishi, ganin yanda suka ruɗe sai ya ƙara tarin yana dafe kirji. Mum ce tace Nawaz ɗauko min wayana in kira doctor... Da gudu ta koma falour ta dauko wayar, sai sannan Aayaan ya ɗan rage tarin da yake yi yana nishi kaɗan kaɗan Fasa kiran likitan mun tayi tana mishi sannu, itama Nawaz duk hankalinta ya tashi.. Shi ko Aayaan sai dariyar zuci yakeyi, domin ba kwarewa yayiba shifa kunyace ta kamashi gashi bayaso a cigaba da maganar shine yayi musu acting.. Ruwan mummy yia bashi a hankali tana mishi sannu, shikuma sai lumshe ido yakeyi. A hakan ya karewa Nawaz kallo duk basu luraba, "Oh ita kuma haka take ta riga canzawa kamar hawainiya? Dazu fa ba haka take ba, Aayaan ke zancen zuci... Mummy ce tace pls kije kitchen ki samomin green tea kinji, A hankali ta miƙe ta nufi hanyar da mummy ta nuna mata, Lumshe ido yayi yana kallonta ta ƙasan ido, mamakin yanda hips dinta suke juya wa yakeyi.. Sai yakejin kamar kar ta shiga kitchen ɗin yayi ta kallon tafiyar, Mummyn ce tace Aayaan kaji tsoron Allah ka dena irin wannan, Ji yayi zuciyarshi ta bada daraammm to ko mummy taga kallon da yakeyiwa Nawaz ne.. Daure wa yayi " mummy me nayi? "Wai kai kanaso ka ɓatawa yar mutane rai sai kuma Allah ya shake wuyan da zakayi wulakancin dashi. Wani sanyi yaji a ranshi da mummy bata ganeba... Mikewa yayi "mum nifa naji sauƙi kuzo muje? Aayann bana wasa dakai nasanka da ɓoye ciwo, baza mu fitaba sai nan da minti talatin lokacin jikinka yayi relaxing kada fa ka manta akwai wani ciwon a hannunka. Ba yanda ya iya, haka ya koma ya zauna a one sitter sofa. Fitowa Nawaz tayi rike da mug, gabanshi ta karasa ta ɗan risina ta miƙa mishi, Ganin yanda sukayi matching take amma taketa addu'ar Allah ya amsa mata kudirin ta.... ~*_MATAR RASHEED_*~✍️*🎀🎀 SARFRAZ🎀🎀* *Episode 28* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Ko kyakkyawan parking mummy bata bari drivern yayi ba ta buɗe ƙofar motar ta fita, cikin asibitin ta shiga tana bi gado gado tana dubawa. Da sauri daddyn sarfraz ya bita, sunata dubawa tare. Har gadon karshe amma babu sarfraz, wani irin kuka mai cin rai ne ya kufcewa mummy "shikenan ta faru ta ƙare" Shima daddy gaba ɗaya gwuiwar shi ta sare, ji yayi kafar shima bazata iya daukarshiba, guri ya samu ya zauna a kasa dirshan. Mummy kuwa sai kuka takeyi duk idon mutane ya dawo kanta... Wani dattijo ne ɗan kimanin shekara sittin ya karasa gurin ta "ƴata kiyi hakuri, kuma kiyi tawakkali sannan ki dauki kaddara.... Allah yana son masu hakuri da karɓar kaddara mai kyau ko mara kyau. Kin manta da kissar matarda ɗanta ya rasu taje har makabarta ta duƙa gaban kabarin tanata rusa ihu, wani mutumi yazo wucewa yace kiyi hakuri idan kikayi hakuri kika dauki ƙaddara sai Allah ya jikansa kuma kema ki samu Rahma. Amma matarnan sai ta ƙiyin hakuri ta cigaba da ihu tana dukan kanta... Sai daga baya ta gane ashe mutumin nan dayace mata tayi hakuri Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ne, Take ta tafi gabanshi ta faɗi tana cewa nayi hakuri ya nabiyy. Murmushi Annabi yayi yace, sanda nace kiyi hakuri dakinyi to shine kikayi hakuri don Allah, amma yanzu darajata ne yasa kikace kin hakura, kuma alokacin danace kiyi hakuri da kinyi to da danki Allah ya saka shi a aljanna kuma kema haka... To ƴata abinda nakeso ki fahimta shine Allah ne ya baki kuma ya amsa to saikiyi mishi hamdala kuma ki dangana tunda wanima ko haihuwar be taɓa yiba, dalilin hakan sai kiga Allah ya Miki wata baiwar ta daban. Wani irin imanine ya shiga daddy da mummy da duk ma mutanen dake gurin, goge hawayen ta tayi tace "baba Nagode Allah ya saka da Alkhairi... Shima daddy godiya yayi mishi sosai sannan suka nufi mutuary don ɗakko gawar sarfraz... Nan ma duka babu gawar da ba'a ɓude musuba amma babu sarfraz babu alamar shi.. Kuka mummy zatayi Daddy yace "kada ki manta da nasihar da aka gama yi mana yanzu, Allah ne kaɗai yasan me hakan take nufi... Shiru mummy tayi sai kuma ta kalli dadyn tace " amma kasan wani abu? Idona ya rufe akan sarfraz sam banma tuna da Nawaz ba, kuma gashi itama babu ita, Dole akwai wani abu.. Daddy yace"to abinda nakeso dake shine kiyi hakuri mu mikawa Allah komai, muriƙa addu'a.. Fita daga asibitin sukayi mummy tanata goge hawaye, cikin motar suka shiga don komawa gida.... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Hassu na nan zaune batada abinyi sai kallon sarfraz, ko fitsari bata iya zuwa tayi saiya matseta saboda kada ta tafi wani abu ya samu Sarfraz. Ta ɗura mishi nono yafi sau bakwai wai kada yaji yunwa.. Anan ta lura wandonshi ya jike, kuka ta fashe dashi "don Allah kiyi hakuri wallahi bansan kinajin fitsari ba dana ɗagaki kinyi... Ruwa ta ɗebo da yawa ta zuba a gurin sannan ta samu zaninta ta ɗora a saman wandon sarfraz sai kuma ta zare wandon ta ƙasa.... Shidai sarfraz babu um babu um'um ko ƙifta idoma bayayi.. Haka ta koma ta zauna tanata kallonshi ''wannan daga ganinta irin ƴan birnin nan ne masu kyau da kwalliya, jifa kayanta har yanzu kamshi sukeyi .. Nonon ita ma ta kamfato a ƙoƙo ta fara sha, don bazata iya barin sarfraz shi kadai ba ta tafi dafa abinci ba, kuma gashi ta fara jin yunwa... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sai da ya kalleta ya ɗaga mata gira ɗaya yace "Nagode" sannan ya amsa tea'n Ɗaya daga cikin kujerun Nawaz ta zauna tayi tagumi... Mummy ce ta kalleta "daughter what is wrong? Murmushin iya baki Nawaz ta ƙaƙalo "babu komai Amma, i am okay.. "Ban yarda ba, wato kema halinki daya da Aayann koh? Kuyi ta ɓoye abu har sai yayi muku illa tukuna za'a sani.. Atare suka kalli junansu, daga mata gira Aayaan yayi tayi saurin kauda kanta... "Waishi wannan Aayaan ɗin saikace tsohon kwarto bini bini ya riƙa daga wa mutum gira.. Nawaz ke zancen zuci Maganar mum ce ta dawo da ita daga duniyar tunani "daughter bakice komai ba? "Ehm mummy au ehm dama babu komai. Aayann dake gefe ne yace "taɓ ai wannan uwar in'inan da kikayi da ace a barrack ne sai kin gane kuranki wallahi.. "Dakata malam! Idan bazaka iya kalloba to kabamu guri, naka ido kada ka kuma sa mana baki a cikin maganar mu. Chuno baki yayi "Allah Sarki Aayaan, Allah ya ƙara baka hakuri, tunda yinka da Allah yayi a jinsin maza ya ja maka baƙin jini ya zakayi, sai hakuri. Buɗe baki mummy tayi tana kallonshi " lallai Aayaan wuyanka ya isa yanka Ni kake kallo kake fadawa maganar da kaga dama ko? To ai idan ka isa ba hakuri zakayiba kamata yayi kawai inga ka zama mace.... Dariya ya kyalkyale da ita "mum idan na zama mace ai abin bazaiyi kyan ganiba wallahi, sunan wani abu wai shi kwaftari.. Dariya Nawaz ta kyalkyale Da ita "mummy ai idan yaya Aayaann ya zama mace wallahi babu namijin dazai aureshi. "Saboda me" mummy tace cikin jin dadin ganin yadda Nawaz ɗin take dariya. " Ai wallahi da wannan jikin nashi mai kama da dutse idan mijin yayi mishi laifi zaneshi zaiyi tsaf, rannan fa ya daukeni amma gudu yakeyi. Buɗe baki Aayaan yayi yana kallonta "kaf dama tana surutu haka? Wow shifa dama yana son macen da zata riƙa yi mishi hira ba wadda zata zauna tayi maka dunkum ba.. ji yayi ta ƙara burgeshi balle da take zance a kanshi tana murmushi... Mummy ma dariya ta kyalkyale da ita " gaskiyar kine Nawaz dama gashi da ƙosawa.. Murmushi Nawaz ta kuma yi "ai mummy Gara kawai yayi zamanshi a namijin shi, zaima fi kyau kuma kinga shi zai bada doka ba bashi za'a yiba... Duk Wannan hirar da akeyi mummy tana binsu ne amma akwai abinda take karanta a bangaren Aayann. Aayaan da baisa bakiba sai lokacin yace " sister ashe kina hira dama? Kunyace ta kama Nawaz sai lokacin abubuwan da ta faɗa suka dawo cikin kwakwalwar ta, ai ji tayi kamar ta fasa ihu.... Mikewa tayi "Amma ina zuwa , bata jira amsar taba tayi hanyar dakin da akace natane da gudu.. Dariya mummyn da Aayaan suke mata.. Mum taji daɗi sosai ganin yanda kowa ke farin ciki "Aayaan nace maka daughter Alkhairi ce a cikin rayuwarmu kaga yanda kowa ke farin ciki dalilin zuwan ta, amma kai sai kai tayin wani kishin banza.... Murmushi yayi "mum ai kece kin Dena kulani sam tunda tazo, ko ɗan abincin da kike bani a baki ma kin Dena. "Oh to Wayace kada kayi aure, da kayi aure matar kace zata rika baka cikin so da kauna... "Mum zaki fara kenan koh? "To nayi shiru, kirata mu tafi tunda naga ga dukkan alamu ka samu sauki.. Mikewa yayi yaje daidai mic ɗin kofar dakin yasa bakinshi a jiki "ki fito mu tafi ko a fasa. Nawaz na zaune taji muryar Aayaan kamar daga sama, ai zunbur ta mike ta gyara rolling ɗin kanta tayi hanyar kofa, Tana budewa sukayi ido huɗu Brown Hazel eye's dinsa ne suka yi mata wani irin kwarjini har saida gabanta ya faɗi da sauri ta kauda kanta gefe, shima abin a bazata yazo mai. Duk mummy na kallon abinda sukeyi "muje" mum tace tanayin hanyar waje. Da sauri Nawaz tace "ya ciwonka? I'm sorry please dalilina kaji, pls kayafemin! Wani daɗi yaji a ranshi" oh wai dama idan aka nuna an damu da kai daɗi kakeji, lallai mu sojoji muna ruwa, sai ka rasa hannu ka rasa kafa amma babu me jajanta maka. Murmushi yayi mata me kyau "kada ki damu da sauki baya min ciwo... Gaba yayi tabi bayan shi cikin sauri... Wata kofa daban taga sunbi bata farkon ba, sai sannan taga ashe wannan itace asalin main door ɗin, wato dazu ta back yard door Suka biyo... Sojoji ta gani duk a ƙame riƙe da bindiga kamar basuda rai. Wata baƙar land cruiser Prado latest series Taga wani soja yayi sauri ya bude gaba da bayanta, Wani ne shima yayi hanyar driver seat zai shiga, Aayaan ne yayi saurin dakatar dashi "No I am going to drive my self. "Yes sir " cewar mutumin yana Sara wa Aayaan Ita dai Nawaz sai ido, da sauri mum ta shiga baya ta kishingiɗa, yunƙurin shiga Nawaz tayi "daughter kije gaba zan ɗan mike kafa ta anan kada jini ya tarun mini. To Nawaz tace sannan tayi side ɗin me zaman banza, Kusan tare suka zauna da Aayaan, sai kuma ƙofofin suka rufe kansu da kansu, take wani sanyi da kamshi me daɗi ya garwaye cikin motar. Key yayi mata ya nufi gate ɗin da dama an wangaleshi tun tuni, sun ɗanyi nisa ta mirror ya hango kamar motoci na binsu , birki ya danna sannan ya buga stiyarin da ƙarfi "mummy kinga guards ɗin can sun biyomu koh? "Ninace su biyomu tunda garin babu kyau, ko kanaso wani abu ya faru damu ne? "Nidai mumy Wallahi nagaji da binbinin nan ace duk inda zaka ana binka ana gadi kamar wani ƙaramin yaro... Amma tunda kince kece shikenan.. Kunna motar yayi suka ci gaba da tafiya... Saida suka dauki kusan awa ɗaya a hanya sannan Nawaz tace "can layin zaka shiga gida na hudu.. Layin Aayaan ya shiga sannan ya duba gida na hudu yayi Parking.. Da sauri sojojin suka zo suka buɗe musu kofofin sannan sukaja gefe suka tsaya Nan yara suka fara taruwa ganin motar sojoji har guda uku, manya kuma so suke suga su waye zasu fito daga motar... Mummy ce tace "daughter ki shiga kiyi mana iso ko! "Ai saimun fara shiga faɗa tukuna kafin mu shiga cikin gidan kinsan shine hakimin garin nan. " Okay to muje" gaba Nawaz ta shiga har gaban fadar, ciki ta shiga ta samu Guri ta zauna, suma su mummy guri suka samu suka zauna. Aayann ne yace "dan Allah ayi mana iso gurin hakimi. Wani bafade ne yace to sannan ya shiga cikin gidan ya isar da cewa baffa yayi baƙi.. Shiru baffa yayi kamar yace ace bazai samu damar zuwaba sai kuma yace " kace ina zuwa" Tafiya bafaden yayi don isar da sakon baffan. Bafffa ne ya miƙe bari naje naji meyasa ake nemana? "Allah yasa Alkhairi ne cewar amma (kakar Nawaz). "Ameen yace kawai ya fita daga ɗakin, Ai be karasa zamaba Nawaz ta mike tayi gurinshi ta rungume shi da karfi tana dariya. "Muryar wa nakeji haka kamar ta Nawwarah? Cikin zumuɗi Nawaz tace "wallahi baffa nice. Sakin shi tayi tace kagani, nice Bai shirya zama ba yaji shi zaune a kan kujerar shi, Alhamdulillah yaketa maimaita wa a cikin zuciyarshi. Sai sannan kuma Nawaz tayi cikin gidan da gudu..... Gaisheshi mummy tayi Sannan shima ya gaisheshi... Da sauri baffa yace "wa nake gani ne sak kamar ɗana Muhammad? Mummy ce ta kalli Aayaan, shima ita ya kalla. A tare suka ce ........... *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 29* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* A tare sukace "Baba wane Muhammad ɗin? "A.V.M Muhammad mai goro, nida babanshi malam Aliyu me goro aminaine irin amincin da ake zama kamar ƴan uwa... Ba irin na yanzu ba Yanzu hakama bamufi awa ɗaya da gama waya dashiba. Amma dai Allah yayiwa Muhammadun da na sani rasuwa, yaron Arziki... Allah dai yayi mishi Rahma, sau biyu yana kaini Saudiyyah. Wani daɗi ne ya ziyarci mummy jin yanda ake yabon mijinta marigayi... Cewa tayi "Ni matar shice wannan kuma ɗan shine sunan shi Aayaan, Da sauri baffa ya miƙo hannu "zo zo zo nan jikana Ayatullah, Allah sarki ashe dai inada wasu ahalin ban saniba. Miƙewa Aayaan yayi yaje gaban baffa yana sussunne kai Akan cinya baffa ya ɗora shi, ai da sauri Aayaan ya miƙe yana murmushi.. "Baffa ai sai in karya maka kafa" Aayaan yace yana murmushi... " Aikuwadai, baba Wannan gabjejen zaka ɗora a cinya? Cewar mummy tanajin farinciki a zuciyarta fadawa dai sai murmushi sukeyi saboda sun daɗe basu ga hakimi yana farin ciki hakaba.... NAWAZ Koda ta shiga cikin gidan da gudu ta faɗa jikin umminta tana farin ciki, Allah na gode maka da kasa na ƙara ganin ummina.. Sakin baki kowa yayi ganin Nawaz tsaf cikin kwanciyar hankali. Nura ne yace "Nawwarah daga ina? Hmmm kawu ai abin akwai tsawo, bari na gama ganin ummina zan baku labari, ina Amma? Ta shiga bayi cewar Nura, wanda a kallo ɗaya zaka fahimci irin farin cikin da yake ciki. Ummi kuwa tama kasa magana domin ganin abin takeyi kamar a mafarki, sai hamdala taketa yi a zuciyarta tana godewa Allah subhanahu wata'ala daya dawo mata da ƴarta sanda ta cire rai da kuma ganinta. Itama Amma da gudunta ta fito daga bayi, Nan ta zauna gefen Nawaz tana jin wani irin farin ciki a zuciyarta, domin bata taɓa zaton zata kuma ganin Nawaz ba. Bayan an kimtsa ne Nawaz ta fara basu labarin abinda ya faru da ita.... Su kuwa acan fada hirace ta ɓarke tsakanin baffa da Aayaan, saboda baffa nata bashi labarin yarintar mahaifinshi... Sai daga baya baffa yace, au farinciki ma yasa na manta komai.. Ga dukkan alamu kune kuka tawo da Nawwarah koh? "Baba Nawaz kake nufi? Cewar mummy "Eh ita nake nufi ƴata, Aayann Mummy ta kalla "son kabashi labarin abinda ya faru. Nan ya sanar da baffa duk abinda ya faru, tundaga farko babu abinda ya ɓoye mishi... Baffa ne keta yi mushi godiya, yana sawa Aayaan albarka, sannan ya ƙara da cewa wannan wahalar da kasha bazata tashi a banza ba, zanyi maka kyauta mai girman gaske, saboda ka dawo mana da farin cikinmu har gida, don haka kyautar guda ɗaya ce tamkar da dubu kuma zata ƙara mana danƙon zumunci.. Mummy ta fahimci abinda baffan yake nufi amma Aayaan ko a takalmin shi, domin shi bema gane me baffa yake nufi ba, shidai abinma dariya ya bashi, wai shi za'a yi wa kyauta. ° A cikin gida kuma Nawaz ta gama basu labarin abinda ya faru da yanda Allah ya kuɓutar da ita... Sunyi farinciki sosai da fatan Allah ya daɗa kiyaye gaba, sannan suka taso don zuwa fada su yiwa su Aayaann godia... Gaba daya fadar ta kaure da surutu, sai daga baya komai ya dawo dai dai, amma daka kallesu zaka gane suna cikin matukar farin ciki... Mummyn Aayaan ce tayi gyaran murya sannan tace "baba da mama da mahaifiyar Nawaz da kuma duk wanda yake da hakƙi akan Nawaz don Allah ina Neman alfarma akan a ara mana Nawaz mu tafi da ita zuwa gidanmu. Saboda dalilin abinda ya faru Governor da sauran ministoci harda yan majalisu suna so suga Nawaz, saboda dalilinta anyi nasarar kama ƴan ta'adda, da kuma ceto rayukan mutane masu yawa.... "Haba ke kuwa" cewar baffa yana kallon mummyn Aayaan, Ai Nawwarah ki dauketa kamar yadda kika dauki Ayatullah, itama ƴar kice.. Amma ma haka tace, kowa ya nuna babu wata matsala hatta ummin Nawaz, dubada yadda suka nuna suna kaunar Nawaz ɗin.... Baffa ne yayi gyaran murya Sannan yace "amma dai bayau zaku tafiba, saboda dare yayi idan Allah ya kaimu gobe sai kuyi sammako.... Dubada yadda baffa ya nunawa Mummy halarci, ga kuma abinda baffan ya faɗa akan Aayaan game da Nawaz yasa taji bazata iya yi mishi musu ba, "To Allah ya kaimu" Shima Aayaan sai murna yakeyi saboda lokaci ɗaya yaji dattijon ya shiga ranshi, ko babu komai zasu kwana suna hira, kuma zai kara sanin cikakken tarihinshi... Nura baffa yasa ya gyara ɗakin baƙi, saboda anan su mummy zasu kwana ... Koda dare yayi mummy sunata hira da amma ita kuma Nawaz alokacin ta samu damar keɓewa da umminta har ta bata labarin sarfraz tun daga farko. Fashewa ummi tayi da kuka "innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, yanzu kina nufin ba'a ga sarfraz ba? Kuma ta dalillinki hakan ta faru? Shiru Mummy tayi tana tunanin yadda zata warware wannan al'amari. Cewa Nawaz tayi kinsan halin baffa idan yaji Maganar nan nashiga uku, yanzu abinda zakiyi shine kiyi ta addu'a, nima zanyi sosai, idan kika dawo daga tafiyar da zakiyi sai mu shirya muje gidansu SARFRAZ ɗin tare da Nura da Amma. Aayann yana can ya buɗe baki da hanci yana sauraron baffa, shiko baffan sai bashi labarin lokacin da kakanshi yayi aure har zuwa sanda aka haifi Muhammad wato baban Aayaan.. Sukuwa guards ɗin Aayaan a cikin mota suka kwana bayan an aika musu da abinci..... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Koda gari ya waye da wuri suka shirya don tafiya, baffa ne ya ƙara kallon mummy yace "ƴata ina fatan zaki bani haɗin kai a ƙudirin dana dauka? Murmushi mummy tayi "Insha Allah baba, nama riga na baka, komai kayi Ni ƴar kace Aayaan kuma jikanka ne.. Aayann ne ya kalli mummy "Mummy wai me kuke magana akai ne nifa ban ganeba? Baffa ne yace "jikana akan ka muke magana akwai abinda zanyi ne, kuma sai kafi kowa amfana da farin ciki da abun... Girgiza kai Aayaan yayi badon ya ganeba.... Har mota suka rakasu suna ta Daɗa yiwa mummy da Aayaan godiya.. Bayan sun tafi haka suka koma gida cike da kewa musamman baffa daya kwana hira da Aayaan, kuma ya lura yarone me hankali da girmama nagaba dashi.. Ko minti goma kwarara basuyi da fara tafiya ba mummy tace wa Aayaan ya Dena driving, Daya daga cikin guards ɗin ta kira tace yayi driving ɗin duba da Aayaan baiyi barciba da dare. Cewa tayi ya koma baya dayake dama ita a gaba ta zauna Nawaz ce kawai a baya... Bayan ya koma ya zauna, itadai Nawaz bata kalleshi ba sai dai gabanta nata dukan uku uku, sannan kamshin turarenshi ya cika mata hanci... Ɗago da kanta tayi aukuwa cikin kuskure suka haɗa Ido, murmushi yayi mata haɗe da ɗaga mata gira ɗaya, da sauri Nawaz ta kau da kai domin itafa abin Aayaan ya Fara bata tsoro, mutum kamar wani kwarto, shi bazaiyi maka maganaba sai dai ya riƙa ɗaga maka gira.. Suna nan zaune Nawaz taga Aayaan yayi barci, ajiyar zuciya ta sauke, domin itama barcin takeji amma bataso tayi saboda shi, ɗan kishingiɗa tayi itama don taɗan rage gajiya aikuwa nan barci yayi gaba da ita. Ashe dama idon Aayaan biyu yana kallon duk abinda takeyi... Zubawa fuskarta ido yayi yana kallonta, gashin idonta wanda ya kwanta luff a fuskarta yabashi sha'awa sai madaidaicin cute lips dinta me shape ɗin heart.... Hannu yasa zai taɓa fuskarta kome ya tuna oho sai kuma ya fasa, Shima dai barci ne yayi gaba dashi dukda shiba gwanin barci a mota bane amma kasancewar kusan kwana uku baiyi barciba yasa barcin ya daukeshi be shiryaba.... "Aayann tunda muka shiga week ɗin nan idan na kira Aseey a waya bana jinta sam, tun ban damuwa wallahi har na damu.... Cewar mummy Shiru taji Bai Bata amsaba, waigowa baya tayi aikuwa nan taga Aayaan kishigiɗe Nawaz kuma tayi pillow da damtsen shi na dama sunata sharar barci abin su... Murmushi mummy tayi ganin yanda sukayi kyau kamar couples, ita dai batada addu'ar daya wuce Allah yasa Aayaan yace yanason Nawaz, yarinyar ta shiga ranta sosai... Ahaka aka isa gida amma basu tashi ba, fita mummy tayi ta shiga ciki sannan tayiwa guards ɗin kashedi akan kada a tashesu a bari su tashi da kansu..... Ashe Aayaan ya daɗe da tashi kunyar mum ce ta kamashi ganin yanda Nawaz tayi nashe nashe ajikin shi, shiyasa ya nuna kamar be tashiba Yana nan zaune yana tunanin yanda zai kwantar da ita ya fita daga motar, ji yayi ta motsa sai yayi saurin maida idonshi ya rufe. Aikuwa da sauri Nawaz ta tashi daga kirjin shi tana salati " Allah yasoni Ni na riga tashi da bansan irin kunyar da zansha ba. A hankali ta buɗe ƙofar zata fita sai jin shu'umar Muryar Aayaan tayi yace "tun tuni na tashi nadai bari ki tashi ne duba da yanda naga kirjin nawa yayi miki daɗi... Ai Nawaz bata iya rufe ƙofar ba ta kwasa a guje tayi cikin falourn.. Murmushi yayi shima yabi bayanta, koda ya shiga falourn babu kowa sai kawai ya wuce dakinshi domin wani irin azababben barci yakeji. Watsa ruwa yayi sannan ya kwanta, ba'a ɗauki lokaci me tsawo ba barci me nauyi ya dauke shi.. Ita kuwa Nawaz Koda tashiga falour itama bataga kowa ba sai kawai tashiga ɗakin da mummy ta nuna mata a Matsayin nata, wanka tayi ta shirya amma kuma ta kasa fita falour saboda bataso koda wasa su haɗu da Aayaan... Hakanan tayi shahada ta fita, cikin ikon Allah kuwa mummy ta gani zata shiga kitchen. "Daughter Ashe kin tashi? "Murmushi tayi "eh Amma na tashi harma nayi wanka.. Okay to ki zauna a falour ki huta zan dafa mana abinci saboda kukun mu taje ganin gida.... Cewa tayi a'a Amma kibari zanyi, "A'a Nawaz kije ki huta" "Don Allah Amma ki bari inyi wallahi ban gajiba" cewar Nawaz tana marairaice fuska.. "To shikenan tunda kin matsa bari na shiga ciki idan kin gama kizo ki min magana. "To Nawaz tace sannan ta shiga kitchen ɗin.... Bayan awa biyu....... Nawaz ce ta wanke hannu tana goge wa a duster... Falour ta fito ta nufi fridge ta dauki ruwa, kai ruwan bakinta keda wuya taji an bude ƙofar falon an shigo. Wata matashiyar mata ta gani wadda a shekaru bazata gaza talatin ba rike da hannun wani kyakkyawan yaro wanda shima bazai wuce shekara biyar zuwa shida ba... Yaron ne ya kwace a hannun maman nashi yayi gurin Nawaz da gudu yana cewa "Aunty Aunty...... Mamaki abin yaba Nawaz saboda itadai bata san matar ba balle yaron, amma sai kawai itama ta buɗe wa yaron hannu ya faɗa kirjinta, take taji wata irin kaunar yaron ta shiga zuciyar ta...... Wallahi na gaji Kuma idan ba'a yi min comments yanda ya dace ba bazanyi update gobe ba. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ🎀🎀* *Episode 30* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji✍️* Cikin falourn matar ta ƙaraso tana murmushi "sannu sister, ina Mummy take? Mamaki ne Ya cika Nawaz, itadai tasan bata san suba amma su kuma sun nuna mata sanayya "tana ɗaki" Nawaz tace tana ci gaba da mamakin wannan lamari Hanyar ɗakin mum bakuwar ta nufa ta shiga ɗakin... "Da alamu waɗan nan ƴan uwa ne na jiki... Mikewa Nawaz tayi rungume da yaron ta shiga kitchen, buɗe warmer tayi ta dibar mishi fried rice din da tayi da yam balls Falour ta fito ta buɗe fridge ta daukar mishi fresh milk sannan ta nufi dakinta dashi... Zama tayi ta riƙa bashi abincin a baki cikin nutsuwa har saida ya nuna mata ya ƙoshi sannan ta bashi fresh milk din yanasha da kanshi. Bayi ta shiga ta haɗa ruwan wanka a jacuzzi Sannan ta fito ta dauki yaron, kaya ta cire ƙoshi sannan tayi cikin bayin dashi. A ciki ta saka shi ta fara yi mishi wanka, ai nan ya fara fachal fachal da ruwan yana watsa mata.. Dariya ta fara yi itama tana watsa mishi, nan wanka ya tsaya aka fara wasan watsa ruwa... Sai farinciki takeji dama gata mayyar yara kuma batada kannai. Da kyar ta lallabashi ya tsaya akayi wankan sannan ta nannaɗoshi a cikin towel ta fito dashi. Cire kayanta tayi saboda gaba ɗaya sun jiƙe sannan ta koma cikin bayin itama tayi wankan. Fitowa tayi daga bathroom ɗin sanye da pink ɗin bathrobe gashinta a barbaje sai ɗigar ruwa yakeyi alamun ta wanke shi, ganin yaron tayi a kwance har yayi barci, itama kawai sai ta samu gefenshi ta kwanta saboda dama tanajin barcin sosai. ° Mummy na zaune taji an turo ƙofa, bata damu da ta waiga ba saboda tasan bazai wuce Aayaan ba, ji tayi an rungumeta ta baya. Ai da sauri ta waigo, wani irin farin ciki ne ya mamaye fuskar mummy ganin first born ɗinta tana yi mata murmushi. "Aseey saukar yaushe? Gaskiya kin tayar min da hankali sosai yau kusan kwana shida kenan ina kiranki baya zuwa, gaskiya kada ki ƙara yimin irin haka. "Mum kiyi hakuri ki bari mu gaisa tukuna, wallahi nayi kewarki har gani nayi jirginmu kamar baya tafiya. "To Aseey na bari amma ai abin ne akwai farbaga, dama ace kina kusa ne sai in shirya inzo amma abu ba'a nan ƙasar ba gari i London kinga ai zuwa sai an shirya. "To mummy kiyi hakuri ba laifina bane, munje wani mall ne siyayyah to wayan na hannun muhsien shine ya manta da ita a cikin folder chocolate a cikin mall ɗin... Babu irin nemanta da banyi ba, sai jiya ina cikin shiri naji doorbell koda na duba ashe keeper din mall ɗinne wai sunje zasu ƙara abubuwa a cikin store ɗin shine suka ganta, to da suka duba emergency information din wayar shine suka ga address ɗinmu.. Hamdala mummy tayi jin kowa na cikin ƙoshin lafiya, sai sannan suka gaisa da tambayan juna bayan rabuwa.... "Mummy wai ko ina sturbborn brother ɗina yake? Dan Allah kada kice min baya gida..... "Hmm Aayaan ɗan rikici, yananan munyi tafiya ne bamu ɗade da dawowa ba shine yake barcin huce gajiya. Cewar mummy tana kallon Aseey cike da ƙauna. Sai kuma tace Aseey ina muhsien ɗin? Murmushi Aseey tayi "Au na manta yana falour gurin Wata beautiful lady, Sai kuma ta rike baki "mummy kada dai kice min bro Aayaan ne yayi aure! "Da dai bakizoba da anyi" "Eye mummy da raina da lafiya ta ina cikin duniyar nan ban mutuba ace ƙanina ɗaya tilo zaiyi aure amma ban saniba... Aseey ta faɗa cikin tashin hankali "Calm down Aseey, ba haka bane nadai yi Miki ne. Sai sannan Aseey ta sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya.... Mikewa tayi "bari naje gurinshi in bashi surprise" Murmushi Mummy tayi mata "Adawo lafia, Ni dama bana shiga abinku saboda yanzu zakuyi faɗa Yanzu kuma zaku shirya, idan mutum ya shiga ma kunya Zai sha... Tana fita ta nufi ɗakin Aayaan da gudu ko knocking batayiba tasa security kofar ta buɗe, dai dai ya fito wanka sanye da Blue Black ɗin bathrobe fuskarshi duk alamun ruwa sai gashin dake kwance luff a faffaɗan kirjinshi sai ƙyalli yakeyi. Tsayawa kawai yayi yana kallonta, mamaki ne da farin ciki suka kamashi lokaci ɗaya, da gudu Aseey ta ƙarasa ta rungume Aayaan, saboda girman jikinshi sai ta zama ƴar ƙarama a gaban shi dukda ita ce yaya "My One And only bro nayi kewarki sosai Wallahi, hannu tasa ta ɗan jamishi kumatu, naga ka ƙara kyau ne "hope mummy tana kula dakai yadda ya kamata? Cikin idonshi ta kalla tana jiran amsar da zai bata, shikuwa Aayaan gira ɗaya ya ɗaga mata bece komaiba... Dukan wasa Takai mishi "Lallai ne Aayaan wato har yanzu wannan ɗabi'ar taka ta ɗagawa mutane gira tananan, Wallahi bakasan yanda kakeyi bane shiyasa kakeyi... Wallahi idan kayi komawa kakeyi sak kamar kwarto, kwarton ma irin wanda ya saba da kwartanci, sannan ta ruga da gudu Binta yayi da gudu shima yana cewa "gaskiya sister kin cuceni wallahi, nifa na rigada na saba bawai inayi da wata manufa bane, kuma Wallahi inaso na Dena Amma na kasa. Hakuri ta bashi sannan ya hakura ya tsaya, "ina Sweet boy ɗina? "Au yana gurin bakuwar mummy, tunda muka shigo ya tafi gurinta. "Au Nawaz? "Ban san sunan taba, wata dai mai kyau sosai. "Eh itace" cewar Aayaan yana basarwa Kallonshi Aseey tayi "bro wace ita? "Sis bari na shirya its a long story. Guri ta samu ta zauna, shikuma ya shiga ciki don shirya wa, Ba'a daɗe ba ya fito sanye da baƙar T-shirt da Blue Black ɗin cinox trouser, gashin kanshi sai ƙyalli yakeyi saboda gyaran daya sha. Ga wani fitinannan kamshi da yakeyi, Ɗago dakai Aseey tayi "hey bro wannan adon yayi yawa kaida ba mata garekaba sai kayita wahalar da kanka, dama ace Kanada matane to saika riƙa samun lada. Murmushi yayi ''Sis yanzu maganar da kikayi kinyi adalci kenan, ache saboda banida mata kada nayi wanka da kwalliya? "To ai kaine Aayaan munjira munjira amma shiru, mummy ma tayi Maganar, tayi maganar!! Har ta gaji ta dena, yanda bamuda Yawan nan kamata yayi ka duba ka samo mana mai hankali a haɗu a rufawa juna asiri. "Sis bawai Auren bane banaso Wallahi yanda mata suka zamane yanzu abin yake bani tsoro. "Kada ka damu muna tayaka da addu'a insha'Allah Allah zai baka mata ta gari fiyeda wacce kake tunani. "Ameen Nagode sosai sis, kitashi muje naƙosa naga muhsien wallahi. Miƙewa sukayi Aseey na murmushi "to mayen yara, Allah dai ya nuna mana naka...... Koda suka fito falour basuga su Nawaz ba, "may be suna ɗaki, muje mu duba" cewar Aayaan yana nufar ɗakin Nawaz.... General password yasa a kofar ta buɗe, tare suka shiga, babu su a falourn sai kawai Aseey ta wuce cikin ɗakin. Kwance ta gansu sai sharar barci sukeyi Nawaz ta rungume muhsien gam.... Murmushi Aseey tayi "wow ko yaushe har suka saba haka? Bin Nawaz tayi da kallo tana mamakin irin farinta (milky white) duk da ita ma fara ce amma ita Golden white ne kalar skin Ɗin su ita da Aayaan... Ga kuma yanayin gashinta, kuma da alamu ba relaxer tasa ba, cewa tayi "ko a ina suka sami wannan yayinyar? "A daji na samota" Abinda Aseey taji muryar Aayaan tace kenan daga bayanta.. Da sauri ta waiga "A daji kuma? Gira ɗaya ya ɗaga mata sannan yace "Eh" "Fita muje, ka wani shigo ɗakin mata, kasan dai ita ba muharramar ka bace koh? Muje main falour ka bani labarin achan... Gaba ya shiga tana binshi a baya. Da ƙarfi tace "tsaya Aayaan" Waigowa Aayaan yayi da sauri jin yanda tayi maganar. Da sauri ta karasa gabanshi ta riƙe hannun shi tana dubawa "bro yaushe kaji Wannan ciwon? Baya son yayi mata ƙarya sannan kuma bayaso yace Dalilin Nawaz aka harbeshi.. "Harboni akayi shine na kare da hannuna" "Subhanallah, Allah Nagode maka! Wallahi don babu yanda zanyi ne amma Sam banason Wannan aikin sojan da kakeyi. Haɓarta ya tallabo "sis calm down, kawai kici gaba da yimin addu'a insha Allah nothing will happen. Riƙe mata hannu yayi zuwa main falour, a kujera ya zaunar da ita sannan ya fara bata labarin yanda suka haɗu da Nawaz..... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sarfraz bawan Allah, yananan kwance kamar kullum, babu um babu um'um. Yauma hassu ce zaune a gefenshi ta zabga uban tagumi kamar yadda takeyi koyaushe. Tunani takeyi anya lafiya kuwa! Tunda suka tsinci sarfraz be taɓayin bayan gida ba ko sau daya. Sanin batada amsa yasa ta hakura sai bandi ya dawo ta faɗa mishi.. A zahirin gaskiya bata taɓa tunanin zata haɗu da wani wanda bata saniba taji tausayinshi haɗe da kaunar shi kaman yanda takeji game da sarfraz ba. Batada sukuni kullum illa tayita Sallah tana yi mishi addu'a akan Allah ya bashi lafiya duk da sallar ma rabi da rabi ce.... Tashi tayi zuwa gabanshi, kanshi ta ɗaga ta sa mishi pillow sannan ta maida kan a hankali, haka take yini tanayi, idan tasa mishi bayan wani lokaci saita cire wai kada ya gaji idan aka kuma daɗewa sai ta kuma maida mishi..... ~To sai dai muce sannu hassu Allah ya bada lada~ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Rufe baki Aseey tayi jin abinda ya faru "tabɗijan wai! Ashe abinda ya faru kenan? Hu um cewa zakayi tsawoncin kwana gareta amma Aida sun ganta sanda ta gudu da harbeta zasuyi... "Wallahi sis Nima Saida naji fargaba sanda na ganta, Wallahi daurewa nayi amma na zata aljana ce saboda bazan taɓa tunanin mutum sai fito daga cikin wannan uban dajin ba.... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Mummyn sarfraz dai a fili ta hakura amma a baɗini kullum idan ta keɓe ita kadai ta rinƙa kuka kenan har sai kanta yayi mata kamar zai rabe biyu, Kullum gidan nasu a cike yake da mutane, ana addu'a akan Allah ya bayyana shi idan kuma ya mutu Allah ya jikanshi kuma yayi mishi Rahma..... Yan islamiyyar su SARFRAZ su Abdul duk sunzo amma da kuka suka fita jin abinda ya faru, Kowa yana tuna yanda suke abubuwan su a makaranta, ga sarfraz dama akwai farin jini da shiga rai, ko Malam Abdullahi shugaban makarantar da yazo Saida yayi kuka... Haka dai kullum gidan yake wasu na fita wasu na shiga..... Daddy kam ya hakura ya fawwalawa Allah komai Nashi, ya amshi kaddara kuma ya ajiye cewa haka Allah ya tsara mishi, haka masoyiyarshi abar kaunar shi ta rasu sanda zata haifi sarfraz sai kuma yanzu shima SARFRAZ ɗin babu, Fatan shi yanda Allah ya musanya mishi da mummy to Allah ya musanya mishi yanzuma da abinda yafi Alkhairi..... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Nawaz ce ta fito daga ɗaki riƙe da hannun muhsien, sanye take da normal riga da zani, kayan sunyi mata das ajikin ta kamar an gwada ta, Shiko muhsien sanye yake da pant suna tafe yana mata rikici waishi zaici chips, "my friend kayi shiru yanzu zan haɗa maka kaji? "Cewa yayi to Aunty muje kitchen ɗin, sam bataga su Aayaann ba saboda hankalinta nakan muhsien gaba ɗaya. Su kuwa tunda ta fito suke kallon dramar da muhsien yakeyi. Ciccibar muhsien tayi suka shiga kitchen... Aseey ce tace "bro kallon ya isa haka. Aayann wanda gaba daya tunanin shi da ruhinshi sun tafi gun Nawaz ne yayi ajiyar zuciya "nifa muhsien nake kallo ba itaba, naga ya wani ƙara girma da wayau, ga wani kyau da yayi. Tsaff Aseey ta gane Nawaz yake kallo kawai dai ya waske ne... Tun bayan fitowar Nawaz Aseey ta gane hankalin Aayaan sam baya gurinta, binibini sai yayi tsaki sai kuma ya kalli ƙofar kitchen ɗin. Ta ɓangaren Aayaan kuma ji yayi yanaso ya ƙara ganin Nawaz gashi Aseey ta Kafa ta tsare kuma shi beso tayi mishi wata fassarar ta daban. Daurewa yayi yace "sis bari nazo, mikewa yayi ya nufi hanyar kitchen ɗin Ya shiga, dai dai ta gama kwashe chips ɗin kenan Aayaan ya shigo.. Kirjinta ne ya fara heaving yana sama yana ƙasa saura ƙiris chips ɗin ya zube Aayaan yayi saurin riƙe plate ɗin. "Meya faru?" Aayann Yace yana karantar Yadda jikinta yake rawa... Idonshi ne ya faɗa kan zoben da sarfraz ya bata, da sauri ya riko yatsan yana kallon zoben.. Ƙiris ya rage ta zabga ihu amma saita tsaya ganin beyi mata komaiba... "Wa ya baki zoben nan" Aayaan yace yana ƙoƙarin cire zoben daga yatsanta..... Sorry for the late update, WALLAHI na ɗan samu matsala ne .... *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 31* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Muryar ta na rawa tace "don Allah kada ka cire. "To ki faɗa min waya baki? "Sarfraz ne ya bani" Sakin mata hannu yayi saboda wani irin zafi da yaji kirjin shi nayi, "right wai waye sarfraz ɗin nan ne? Nifa da mukaje gidanku babu wanda yayi maganar wani sarfraz, ke kaɗai kawai akace kin tawo ba tare da wani ba. Kuma Ni sam na manta ban tambayesuba, amma bari na kira wayar baffa in tambayeshi yanzu.. "No don Allah kada ka kirashi" Nawaz tace jikinta naci gaba da rawa. "So tell me who is he idan bakya so na kirashi. "Dalibinane" tace a takaice Wani abu Aayaan yaji ya tokare mishi wuya ga idonshi har wani yaji yaji yake mishi, shi kanshi ya rasa meyasa hakan. Da kyar ya Iya daurewa yace "look Nawaz ba wasa mukeyi ba please be serious waye shi? "Allah dalibinane" "Idan shi dalibinki ne ya akayi ya baki zobe kuma kikasa a yatsanki? Sannan kuma ya akayi kuke tare dashi sanda zakizo garinnan? Hawayene ya zubo mata a fuska "bazaka ganeba Wallahi ɗalibinane kuma zoben da kanshi ya bani sannan sanda zan tawo shima kakanninshi anan suke zai zo gaishe dasu shine muka taso tare. Zubar hawayen Nawaz yana dai dai da kamar an zubawa Aayaan garwashi a cikin zuciyarshi. "Look bance kiyi min kukaba, daga na tambayeki? So i am sorry kawai dai ina so na sanine saboda zoben yanada dogon tarihi a rayuwar mummy na. "Mummy kuma? Nidai sarfraz ne ya bani Wallahi ba na mumy na dauka ba, bana daukar abin mutane . "A'a calm down mana meyasa kike da saurin rudewane? I don't mean na mummy kika dauka, dama ai zoben guda biyu ne, amma ki bari yanzu zan kira mummy sai tayi Miki bayani... Tafin hannunshi ta kalla ganin ya cire bandage ɗin sai ciwon yayi wani irin pink, wani zafi taji a zuciyarta ganin yanda yakeshan wannan azabar a dalilinta. "I am very sorry naga ciwonka is still new, sannu yana maka zafi koh? "No never mind, Kim manta ni soldier ne? Ai wannan ba wani abu bane aguri na, Wallahi mantawa ma nakeyi dashi... Kallonshi yakai kan muhsien wanda ya miƙe ƙafa a kasan tile's sai cin chips ɗin shi yake yi hankali kwance... Tsugunawa yayi dai dai shi "Superman babu magana ne? Chuno baki yayi "bakai bane kaketa yiwa Aunty faɗa, kumani ina sonta saboda Nima tana sona. "Oh no ba faɗa nayi mata ba, kawai dai na tambaye tane. "Ba har tears naga suna rolling a cheeks ɗinta ba, kuma babu ruwana dakai tunda kasa Aunty na tayi kuka.... Janyo shi yayi zuwa kirjinshi "i am sorry bazan kuma ɓatawa Aunty ranta ba. "To ka bata hakuri" muhsien yace yana ci gaba da cin chips ɗin shi hankali kwance. Juyawa Aayaan yayi daidai Nawaz ya haɗa hannunshi guri ɗaya "Aunty Don Allah kiyi hakuri bazan kuma ba... Da sauri Nawaz tace "please ka bari yaya Aayaann " Ji yayi kamar babu wanda ya kaita iya pronouncing ɗin sunanshi. Murmushi muhsien yayi "yauwa to yanzu Nima na hakuri, ɗauke Ni muje falour to. Sunkutar shi Aayaan yayi suka nufi falour, sai sannan Nawaz taji ta fara samun nutsuwa. Ta rasa meyasa idan Aayaan yana kusa da ita take neman natsuwarta ta rasa ga wani uban tsoronshi da takeji sannan zuciyarta tayita bugawa. A hankali take tafiya ta fito daga kitchen ɗin rikeda ragowar chips ɗin muhsien. Aunty kinga uncle ya cinye min chips ɗina Koh? Muhsien yace yana kwaɓa fuska kamar zaiyi kuka... Ganin Aayaan zaune kusa da Aseey yasa ta gane yar uwar shice saboda sunyi kama sosai. A ɗan ɗarare tace ''kayi hakuri ga ragowar na ɗauko maka" Ɗan gaban Aseey ta ƙarasa ta risina "ina yini Aunty! Ɗazu bamu gaisaba.... Cikin fara'a Aseey ta amsa da lafiya sister ya hidima da muhsien? "Haba dai Aunty wace hidima kuma, wallahi Ni sabgar yara sam bata damuna... Aseey kuma jin wani irin kaunar Nawaz tace tana bin jikinta.... Murmushi tayi ai muhsien ɗin ne akwai rigima me iya mishi sai Allah... Hamma tayi alamun tana jin yunwa "ohh gaskiya yunwa nakeji wai ina kuku ne? Aayann wanda tun dazu bece komai ba amma yanajin abinda sukeyi sai sannan yace "ta tafi ganin gida. "Yanzu don Allah shine tunda nazo baka faɗa minba? Aida tuni nayi mana girki.... "Wallahi Aunty Nima fa yunwar nan nakeji babu yanda sanyi ne, kuma mummy bata tashiba nasan da tuni ta girka mana wani abuu. Kallonshi Nawaz tayi "nayi girki fa tun dazu, yana dining Nasha ma ai kunci! Ai da gudu Aayaan da Aseey suka nufi Hanyar dining ɗin har suna bangaje muhsien... Aayann ya riga zuwa, beyi wata wata ba ya bude warmer ɗin ai take wani aroma mai daɗi ya bigi hancin shi. Daya warmer ɗin ya buɗe itama yamballs din suma sai kamshi sukeyi. Plate yaja ya zuba fried rice din da yawa sannan ya dora yamballs uku a gefe... Dinner bowl ya buɗe don ganin meye a ciki, ai kuwa coleslaw yagani yaji uban mayonnaise da ketchup.... Ƙara ɗiba yayi ya zuba sannan yaja kujera ya zauna, diba yayi ya kai bakinshi... Wow wani irin daɗi ne ya ziyarci kwakwalwar shi har saida yaji kamar kunnenshi na motsi.... Aseey sai korafi takeyi "shine ka zuba iya naka baka zubamin nawa ba.. "Sorry kawai ya iya ce mata yaci gaba da tura abincin. Itama dai ta gurin Aseey abinda ya faru kenan, amma ita ta kasa boyewa "Nawaz zo" A hankali Nawaz ta ƙaraso dinning area ɗin "gani Aunty" Wata lomar Aseey ta daɗa kaiwa baki, Saida ta cinye tace "sister da gaske ke kikayi girkin nan? Murmushi tayi "eh Aunty Ni nayi" " Masha Allah shin a taba faɗa Miki in iya girki me daɗi? Hmm wallahi abincin nan yayi mini daɗi fiye da yanda kike tunani.. Itadai Nawaz sai murmushi takeyi, goga Aayaan be kula suba sai faman aikawa tumbin shi yake yi. Cikin falourn Nawaz ta koma ta barsu suna cin abincin... Aayann haka yabar abincin badan ya ƙoshi ba sai don ya gama cika tumbin shi fam.... Nawaz na kitchen tana kokarin haɗawa muhsien smoothie taji kamar anyi mata rumfa, ile kuwa Aayaan ne tsaye a bayanta yana murmushi. Da ƙarfi kirjinta ya buga, sai kuma jikinta ya dauki rawa.... Duk abinda take yi Aayaan na kallonta, matsowa ya daɗa yi yazo gaf da ita sosai, har yanajin numfashinta na sauka a wuyanshi Ita kuwa Nawaz ji take kamar zata shiɗe saboda fargaba ga kuma kamshin turarenshi daya gama cika mata hanci. Cikin soft husky voice dinshi yace "meyasa kikejin tsoro na? Koni dodo ne? Wani miyau nte gishiri Nawaz ta haɗiye amma ta kasa cewa komai... Ƙasa yayi da kanshi dai dai kunnenta yace "ki faɗa min Ni dodo ne? Ko zan cinye kine? Tsigar jikintane taji duka sun buɗe ai da sauri tace "a'a wallahi kai ba dodo bane don Allah kayi hakuri ... "Meyasa zaki bani hakuri? Kinyimin laifi ne? Cikin rawar murya kamar zatayi kuka tace "Ni dai don Allah kayi hakuri kuma ka matsa kusa dani... Murmushi yayi ya Kara matsawa kusa da ita saura ƙiris jikinsu ya haɗu... Ihu Nawaz ta saka da karfi haɗe da rufe idonta, domin ji tayi numfashinta na sama na ƙasa... Aseey dake falour a zaune ta taso da gudu ta shigo kitchen ɗin "meya far...... Makalewa maganar tayi a maƙogoranta ganin Aayaan tsaye gaban Nawaz, ita sam batasan sanda ya shiga kitchen dinba, tasha ma Nawaz ɗin ta ƙone ne. Malam matsa ka bani guri, kazo kana tsorata yar mutane, hannun Nawaz ɗin ta kamo "zo muje sister rabu dashi kinji... Falourn suka koma dai dai mummy ta fito "daughter meya sameta naga kamar jikinta na rawa, mummy tace tana nufosu "Wallahi Mummy Aayaan ne yaje ya firgita ta" "Ayyah sorry my dear, ki barni dashi zan saɓa mishi sosai..... Fitowa Aayaan yayi daga kitchen ɗin rike da smoothie ɗin da Nawaz ta haɗawa muhsien yana sipping. "Zo nan mara kunya! Me kayi mata? Mum tace tana zabga mishi harara Murmushi yayi "mummy ni banyi mata komai ba, kawai dayake banyi sallama bane shine ta firgita. Kallonshi Nawaz tayi cikin mamaki "kashe mata ido yayi hade da ɗaga mata gira yana yi mata wani shu'umin murmushi... "To wallahi kada ka kuma, kaji na faɗa maka, Kafi kowa sanin nawaz amana ce a gurina. "Wallahi Mummy Aayaan mugune, kada ki yarda, Nima don yayar shice shiyasa babu yanda ya iya dani.... "Ke yayar shice" cewar Nawaz da ita kanta batasan sanda maganar ta kufce daga bakinta ta fito ba .. Dariya Aseey tayi "Wallahi Ni yayar shice, kada ki ganshi gabjeje haka shekara uku na bashi.... Kinga shekarata 36 shi kuma 33.... Murmushi Nawaz tayi "tabɗijan wai da gaske kike? Ita tama manta da abinda ya faru gulma na cinta aciki..... Aayann ne yace nifa banason raini, aiko makaho ya shafa zai gane gaskiya.... Jin Muryar Aayaan da Nawaz tayi ne ta dawo hayyacinta, ai da gudu tayi hanyar dakinta Sukuwa suka kwashe mata da dariya..... Guri mum ta samu tana ci gaba da murmushi, domin abinda Nawaz tayi ya bata dariya... Shiko Aayaan gefen mummy ya zauna yana cewa mun i have a Great news for u, amma saikin biya. " Zan biya ko nawa kayi demanding! "Mum na samo Miki biyuninki" cewar Aayaan yana kallon mummy Da sauri mummy ta mike "Aayaan put joke apart, don Allah da gaske kake? "Mum wallahi dagaske nakeyi? Itama Aseey mikewa tayi "bro kasan mummy bata wasa da wannan maganar don Allah da gaske ne? Kada fa ka bata mata rai ... Hannun mummy ya kama yace "zo muje mummy ki gani da idon ki... *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 32* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Hanyar dakin Nawaz yabi da mummy, suna zuwa ya buɗe security yana riƙe da hannun mummy suka shiga dakin... A zabure Nawaz ta miƙe ganinsu duka, gani takeyi kamar tayi musu laifine .. Direct gaban Nawaz ya ƙarasa, ya zuwa ya kamo hannunta yana nunawa Mummy "kin ganshi mummy, Wallahi shine domin bazan taɓa mantawa da zoben nan ba, saboda kullum saikinyi magana akansa. Ita kuwa Nawaz jin abinda Aayaan yake faɗa take fargaba da tsoro suka kamata, durkushewa tayi a gurin tana sakin kuka, "mummy wallahi billahilazeem ban ɗaukar Miki zoben kiba, Wallahi sarfraz ne ya bani. Ɗagota mummy tayi "yi shiru mu daughter baki daukar min komaiba na sani, shima Aayaan ɗin ne be iya bayani ba. " I'm sorry" Abinda Aayaan yace kenan yana kallon Nawaz.... Hannunta mummy ta rike ta kaita saman sofa ta zaunar da ita.... "My daughter ki zauna anan bari naje na ɗauko Miki nawa zoben yanda Zaki fi samun nutsuwa" Fita mummy tayi ba'a fi minti biyar ba ta dawo rike da zobe a hannunta, suko Aseey da Aayaan zaune suke babu wanda yake iya magana burinsu nawaz ta basu labarin abinda ta sani game da zoben. Daughter kinganshi! Sunyi kama koh? Ciro naki mu gani ko akwai banbanci... Da sauri Nawaz ta zare zoben a hannunta ta mikawa mummy, duddubawa mummy tayi sosai zoben irinsu daya har takai mummy bazata iya gane wannene nataba a ciki.. Hannu mummy ta haɗa guri ɗaya sannan ta durkusa "my daughter don daraja da girman Allah ki taimaka ki faɗa min gaskiyar labarin zoben nan, wallahi tun tsawon rayuwata banida addu..... Da sauri Nawaz ta riƙe mummy tana ɗago da ita, "haba mummy meyasa zaki duƙa mini? Kuka Mummy ta fashe dashi "don Allah ki taimaka min wallahi kullum addu'a ta bata wuce inga zoben nan da kuma wanda zoben yake a hannunshi..... "Mummy don Allah kidena kuka, zan kaiki har gidansu SARFRAZ ɗin inyaso saimuji ko iyayensu sun san labarin zoben, amma wallahi Ni bansan komai gameda zoben ba, har gida yazo ya kawomin sanda sukayi min laifi a makaranta saboda nace bazan kuma zuwaba.... Aseey da Aayaan babu wanda ya motsa domin sun san mummy zata iyayin fiye da haka ma saboda ba'a yini guda batayi maganar zoben ba, har ce musu takeyi su riƙa lura da hannun mutane koda zasuga me irin zoben...... Sai dai duk da haka hawayene yake zuba a fuskarsu, ganin halinda mummyn ta shiga lokaci guda... Tasowa Aayaan yayi Ya rungume Mummy "we are sorry mum, Insha Allah komai ya kusa zuwa ƙarshe tunda har Allah ya aiko Miki da zoben har gida... Yanzu duk mu shirya zuwa gobe Insha Allah zamuje chan Zaria ɗin sai muji ko su iyayen sarfraz ɗin sunsan wani lamarin daya shafi zoben.... Sai lokacin itama Aseey tasa baki "mum ayi yanda Aayaan ɗin yace, mu shirya goben sai sister Nawaz ɗin ta rakamu... "To shikenan Allah ya kaimu" cewar mummy tana goge hawayen fuskarta.... Ɗan matsawa Nawaz tayi Saboda yanda turaren Aayaan ya cika mata hanci.... As usual kallonta yayi ya ɗage duka girarsa biyu alamun tambaya.. Itakam batabi ta kansaba illa kanta data kauda gefe domin ita a yanzu ta riga da ta saba da wannan ɗabi'ar tashi.... Aseey ce ta riƙe hannun mummy "mum zo muje kici abincin da Nawaz ta dafa wallahi bakiji dadinsa ba.. Murmushi mum Tayi "to muje kinji girkin ƴar tawa ya yayi" a tare suka fita falourn harda Aayaan. Ajiyar zuciya Nawaz ta sauke "menene alaƙar mummy da zoben nan? Hmm yanzu da ace ma na wani mugun abu ne dana Banu, daga bani abu nasa a hannu ban san kona meye ba.. Tuna a abubuwan da suka faru tsakanin ta da SARFRAZ tun daga lokacin da suka hadu har zuwa rabuwar su tayi, wata irin sabuwar damuwa ce ta ziyarci kwakwalwar kanta, a zahirin gaskiya ita dai tasan batason SARFRAZ duba data girmeshi sannan kuma tana matukar jin tausayinshi da mutunta shi, saboda daba don shiba da yanzu ita kadai tasan halinda take ciki.... Tafi minti talatin anan kwance tana tafka tana warwara, turo ƙofar da akayi ne ya dawo da ita Daga duniyar tunanin data faɗa, da sauri tasa hannu ta goge hawayen da suka gangara ta gefen fuskarta... Ɗagowa tayi don ganin ko waye ya shigo, Aayaan tagani riƙe da waya ya nufo inda take, miƙa mata wayar yayi yana murmushi "dadynkine colonel yace yanaso kuyi magana.. A ɗarare ta amshi wayar ta kara a kunne sannan ta furta kalmar "Assalamu alaikum" cikin nutsuwa Ta can ɓangaren colonel yace "wa'alaikis salaam daughter na, fatan kina lafia? Murmushi tayi "lafiya lau Alhamdulillah ya aiki, yasu mama? "Lafiya lau daughter, dama munyi magana da Aayaan ne akan nanda kwana uku zaku tawo Abujan, saboda ayi komai a gama. "To shikenan babu komai Nagode. "Yauwa daughter babu wata matsala koh? "Eh babu"nawaz tace tana daɗa yin murmushi "Okay to ba Aayaan wayar, miƙa mishi tayi sannan ta nufi hanyar bathroom, da sauri Aayaan ya riƙe mata hannu Aikuwa don dole ta tsaya, dama ita babu abinda zatayi a bayin kawai zata shiga ne don gudun Aayaan ɗin. Sallama sukayi da colonel ɗin Sannan yasa wayar a cikin aljihu... "Wai meyasa kike guduna? Nawaz ta tsinci Muryar Aayaan a Cikin dodon kunnenta. "Ko nayi kama da dodo ne? Ita dai Nawaz har jikinta ya fara rawa as usual, kuma still ta kasa cewa komai... "Juyo ki kalleni, ina tambayarki shine kikamin shiru? Rau rau tayi da idonta zata fara kuka "don Allah hakuri... "Oh gosh wai ke meyasa in cika ba mutum hakurine" " Cewa nayi fa kawai ki juyo ki kalleni, amma sai ya zama abin kuka? " Juyo ki kalleni! If not I will do som....... Cikin sauri Nawaz ta juyo ta fuskanceshi amma bata kalli fuskar shi ba...... "Good girl! Tunda kin juyo to ɗago kanki ki kalleni" Gum Nawaz tayi, ita bata ɗago ta kalle Shiba sannan kuma bata bashi amsaba. Murmushi yayi yana ƙara matsowa sannan yace "okay then, i will do....... Nawaz bata jira ya karasa ba ta ɗaga kanta sama ta kalleshi, Domin tasan Duk Abinda zai faɗa ma ba Mai daɗin ji bane, cikin Sa'a kuwa suka haɗa Ido Sosai Aayaann yake kallon ƙwayar idonta wanda dama ita yakeson gani, Saboda tunda suka hadu bata bari su hada ido, illah dai ta kalli fuskar shi. Saurin kau da idonta tayi ganin cikin ƙwayar idon Aayaan ɗin cike take da abubuwan da bata gane musu ba, sannan colour din iris ɗin shi grey ne saɓanin tata da take baka..... Wani shu'umin murmushi Aayaan yayi, yau ya dauke duk wani abu da yakeji kuma yaga abinda yakeso ya gani, duk sanda yaga Nawaz sai yaga idonta kamar cike yake da hawaye har yake tunanin ita me yake sakata kuka koda yaushe, but yanzu ya gane ba hawayebane ashe tanada bold and oil lense ne, shine yake sawa yaga kamar hawayene a idonta. Still kuma ganin Black iris ɗinta ya burgeshi, saboda babansu Black iris gareshi amma basuyi irin nashi ba sai sukayi irin na mummy.... Gwauruwar ajiyar zuciya ya sauke sannan yace yace "i don't know why, but har dai ina tare dake nakan jini cikin nishaɗi sannan nakan manta komai, So yanzu ki samo min amsar wannan, zuwa gobe kafin mutafi zan tambayeki. Wani shu'umin murmushin ya daɗa sakin mata sannan yayi hanyar fita yana cewa "You are so special and different.. Nawaz sumar tsaye tayi saboda maganganun sunyi mata nauyi sannan ga wani abu daya kuma sata, wai ta nemo mishi meyasa yakejin nishaɗi duk sanda suke tare. Lallai wannan kakan sarfraz ne a Rashin ta ido, wato shine yake jin abu amma ita zata nemo mishi amsa, Tabb wallahi wannan ɗan rainin sense ne.... Komawa tayi ta zauna a gefen gado, gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, ita wallahi zaman gidan nan ya isheta, ga kuma wani uban tsoron maza da yake ƙara ɗarsuwa a Cikin zuciyarta... Tsaki tayi sannan ta shige bayi.... ° Aayann kuma koda ya koma ɗaki kasa yin komai yayi "ya faɗa duniyar tunani, shidai tun first time da yaga Nawaz yaji ta burgeshi yanda tayi jarumtar guduwa daga hannun ƴan ta'addan nan, yanaso yaga mace self difendent balle yanzu daya zauna da ita ya ƙara sanin halayanta. Ya lura bata son magana, kuma ta cika tsoro da jin kunya, tanada son yara bugu da ƙari kuma akwai kyautatawa duk wanda ya raɓeta... Murmushi yayi yana tuna tsoro irin na Nawaz, dramar da suka gamayi yanzu ne taketa dawo mishi. Sai kuma ya ɓata fuska "but zanyi missing ɗinta idan ta koma gida" Take yaji wata irin fargaba ta dirar mishi a zuciya, ga wani bugawa da kirjinshi yakeyi da sauri da sauri, mamaki abin ya bashi domin be taɓa tsintar kanshi a irin wannan halin ba. ° Koda Nawaz ta fito daga wanka guri ta samu ta zauna bata wani yi kwalliya ba illa dai ta tashi ta samu yar doguwar riga mara nauyi ta saka, Sannan ta ɗora hijab akai tayi sallah, falour ta fita ta shiga kitchen ta ɗebo abinda zatasa a bakinta saboda bata ci abinci ba tun wanda suka ci a gidansu baffa kafin su tawo.. A tsakiyar falour sukayi kiciɓis da Aseey itama zataje kitchen ɗin "A'a sister har kin tashi daga barcin? Murmushi tayi bata Bata amsaba sai tace ina muhsien? "Ai tun ɗazu dayayi barci be tashiba, yana can shida Mummy.. Murmushi Nawaz ta kumayi "Allah sarki ai Gara ya huta, barin gobema zamu kuma ɗaukar wata tafiyar mai tsawo.. Nawaz nakai aya Aayaan yana fitowa daga ɗaki, da sauri ta nufi hanyar dakinta har tana hardewa... Sakin baki Aseey tayi , meke faruwa tsakanin waɗan nan kuma, kamar tsoronshi takeji fa? Shiko Aayaan sanin saboda shi ta nufi hanyar ɗaki yasa da sauri yace "sister please kada ki shiga ɗakin nan, don Allah zoki haɗa min smoothie ɗin da kika haɗa wa muhsien ɗazu... Ja tayi ta tsaya sai kuma a hankali ta juyo ta nufi hanyar kitchen ɗin, ajiye abincin tayi a saman center table ɗin dake tsakiyar ɗakin tayi zata shiga kitchen ɗin... Dakatar da ita Aseey tayi "zauna kici abincin kafin kiyi koma meya saki, ɗazu bashi ya shanye na muhsien ɗin ba .... Da sauri Aayaan yace ayya bansan abinci zata ciba, kawai ma ta barshi haɗe da karasowa cikin tsakiyar faloun yana zama a two sitters couch ɗin dake kallon center Nawaz.... Nawaz dai cewa Aseey tayi auntie bari na haɗa mishi ai babu wahala, kinga sai in tafi ɗakin gaba daya inaso na kwanta.... Wani daɗi Aayaan yaji domin dama saboda ita ya fito sai gashi kuma Allah ya haɗasu... Kitchen ɗin ta shiga yana biye da ita a baya kamar jela, Babban deep freezer ɗin dake cikin kitchen ɗin ta buɗe ta ɗebo iya fruit ɗin da zatayi amfani da shi... Yana tsaye yana kallonta har ta gama haɗa mishi, mika mishi tayi "gashi na gama Saida safe.... "Nagode, good night and sweet dreams..... Bata bashi amsaba ta wuce ya fita daga kitchen ɗin.... Cewa Aseey dake zaune tana kallon zee world tayi "auntie Saida safe zanje na kwanta..... " Okay dear sweet dreams, good night. Ɗakin ta shiga sannan ta samu Guri taci abincin ba Wani da yawa ba saboda tana fargaban me gobe zata tarar a zaria.... Kuma tana tunanin kada mummyn sarfraz tace ita tayi sanadiyar ɓata ko mutuwar ɗanta ... Ahaka Sarkin ɓarayin duniya ya lallaɓo ya saceta bata saniba ... Tunda Nawaz ta tashi sallar asuba bata koma ba, kitchen ta shiga ta haɗa musu break fast da kuma snacks ɗin da idan suna hanya zasuci, tunda tafiyace me nisan gaske .... Saida ta gama sannan ta shirya tanata addu'ar Allah yasa Kada Mummyn sarfraz ta tsaneta.... Aayann ne ya fara fitowa, ganin warmers yayi manya a saman center table, zuwa yayi ya buɗe yana tunanin meye kuma a ciki? Egg roll ne da meat pie 🥧 harda cake 🍰 cike a cikin warmer ɗin.. Ɗayar kuma soyayyen Irish ne da plantain sunata turiri.... Be jira komaiba ya nufi dining ya ɗauko mug da karamin plate ya dawo, Black tea ya haɗa sannan ya duba abubuwan da suka mishi ya Fara ci yana murmushi, ko ba'a faɗa mishi ba yasan wannan aikin Nawaz ne, domin yasan Aseey bata cika tashi da wuri ba balle kuma yau jiya ta iso ƙasar dole tayi barcin gajiya.... Hamdala yayi bayan ya gamsu da abincin sannan ya miƙe ya koma ɗaki don shirya wa, Aseey ce ta fito a firgice "Wallahi sam na manta zamuje wani guri, gashi har takwas ta kusa ba'a dafa komai ba balle mu tafi, muda zamuyi sammako.... Turus ta tsaya ganin Manyan kuloli a Saman table sannan ga mug da plate a gefe alamar anci wani abu, da sauri ta ƙarasa ta buɗe kulolin. Da gudu ta koma dakin mum tana cewa mummy Wallahi she is the perfect match, Allah dai ya tabbatar mana da Alkhairi.... Mum taji daɗi sosai bayan Aseey ta faɗa mata ai Nawaz har ta gama komai. Sai shi mata albarka takeyi taba ƙara jin wata kaunar Nawaz a Cikin zuciyarta... A gurguje suka ci abincin sannan suka shirya zuwa falour, oga muhsien kuwa ihu ya riƙa yi waishi Aunty ce zatayi mishi wanka da kyar ya yarda... A falour suka tarar da Aayaan ya zuba uban ado sai ƙyalli da tashin kamshi yakeyi, Aseey ce ta kalli mum suka haɗa Ido sai kuma suka kyalkyale da dariya a tare .. Tsaf yasan dashi suke amma sai ya basar be tanka musu ba tunda ya lura kwana biyu sunsa mishi ido. Da gudu muhsien ya ƙarasa gurinshi Yana cewa "Uncle kayi kyau, Aseey kuma taje ta kira Nawaz... Godiya sosai mummy tayi mata na abincin data dafa. Ita dai Nawaz nata iya murmushi ne... Tsaff suka tarar da securities ɗin sun shirya, har sun buɗe musu kofofin motar da sauri Aseey ta shige baya tana murmushin da ita kadai ta san manufar shi. Mummy ma zama tayi abayan. Nawaz kuma sai ta tsaya tayi shiru ita gaskiya batason zama a gaba barin tasan Aayaan ne zai tuka motar .. Saurin zuwa gaban mummy tayi tace mummy bari naje waccan motar kawai kinga nan bazai ishemuba kinga ya Aayaan zai zauna a gaba Sannan ga driver kuma kinga ga muhsien.. "Haba daughter kizo mu zauna mana anan, ya za'ayi ki tafi ke kaɗai ... A'a mummy kada ki damu, saurin buɗe motar bayansu tayi ta shiga Domin ko banza ta samu ta sake tayi baccinta son ranta. Tana shiga shima Aayaan ya mikawa Aseey muhsien ya Kalli mummy yace Nima bari na shiga waccan ɗin kawai kada a barta Ita kaɗai kinsan baƙonka annabinka... Be jira me zataceba yaba driver's ɗin umarni sannan ya buɗe baya inda Nawaz take ya shiga, daskarewa Nawaz tayi tana kallonshi cikin mamaki... Suma can mummy da Aseey ne ke mamakin wai yaushe Aayaan ya zama haka, Lallai kam soyayya bata ɓuya, mummy kam sai farinciki takeyi domin zatafi kowa jin daɗi idan Aayaan da Nawaz sukayi auren soyayya.. A ɗaya motar kuma Aayaan ne yaketa yiwa Nawaz wani shu'umin murmushi "nasan Saboda Ni kika gudo wannan motar shiyasa Nima na biyoki, kuma yanzu ina sauraren ki ki bani amsar tambayar danayi Miki juya inba hakaba kuma na......... *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ🎀🎀* *Episode 33* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Jin abinda Aayaan yace yasa Nawaz tayi saurin matsawa gefe ta bashi tazara sosai. Matsawa kusa da ita ya ƙarayi "so kin yarda inyi Miki duk abinda naga dama kenan? Kwaɓe fuskarta tayi "nifa ya Aayaan don Allah kayi hakuri, Ni bansan meyasa ba, kuma Ni wallahi kunya kake Sawa inaji. Ta karashe zancen cikin Muryar shagwaɓa Wadda ita batasan ma tayiba. Murmushi kawai Aayaan yayi "shikenan nabarki yanzu but ya zama assignment, zaki nemomin amsar bayan mun dawo gida..... Nawaz kuwa mamaki abin ya bata "wai inmun dawo gida, sai aka ce mishi a garin zanta zama kenan. Komawa tafiyar kurame akayi saboda babu Wanda ke cewa ɗan uwanshi ƙala. Kowa akwai abinda yake saƙawa a zuciyarshi..... Cikin husky voice dinshi taji yace: naga kamar kinajin barci, ko in gyara Miki kirjina ki kwanta akai naga you feel safe there, saboda rannan ma har muka dawo gida baki tashiba. Ruɗewa Nawaz tayi, sam ita bataso yanayi mata haka, a yanzu gani takeyi ma Aayaan yafi SARFRAZ rashin ta ido.... "Ni banajin barci, Nagode. Shiru Aayaan yayi ganin beci sa'ar neman zance ba, saboda katse maganar tayi bata yarda Tayi tsawo ba.... ° Achan ɗaya motar kuma mummy ce keta murmushi. "Mum what's good? Naga kinata murmushi ne, cewar Aseey wadda ke sonjin ƙarin bayani daga bakin mummy. "Wallahi daughter wani ci gaba naga yanata samun mu. "Mummy wane cigaba ne, cewar Aseey cikin son jin amsar mummy ta gaba. Mummy tace "Aseey Kinga tun randa Allah ya haɗa fuska ta data Nawaz naji wata irin ƙaunar ta acikin zuciya ta, kuma take nayiwa Aayaan sha'awar ta a matsayin mata kuma cikin ikon Allah da mukaje chan gidan kakanninta sai na lura kakanta baffa yanamin hannunka mai sanda, yana nunamin zai ba Aayaan ɗin Auren Nawaz amma sai an shirya... "Kai kai kai Alhamdulillah, Allah yasa hakan ya faru, domin idan haka ya faru sainafi kowa jin daɗi domin naga Nawaz ɗin akwai hankali da kunya. Numfasawa mum tayi "kuma abinda yasa nakejin daɗin, baya wuce ganin Aayaan yana nuna zumuɗi akanta. To amma dai bansan manufarshi ba. Aseey tace "mum amma gaskia akwai matsala. Da sauri mum tace"Aseey wace matsala ce kuma? " Kada ki tada hankalin ki mum, bawai wani babban abu bane, na lura da wani abune daga gurin Nawaz ɗin. Mum ce tace "Ƙaniyarki Aseey wato Ni kike jawa rai koh? Come"on zaki faɗa min ko kuwa saina saɓa Miki! Wai dama gani nayi Nawaz na mugun jin tsoron Aayaan, kuma ko yanzu ma saboda shi taƙi shigowa motar nan, Gashi kuma ya bita.... "Tsoro kamar ya? Cewar mum tana kama haɓarta Gyara Zama Aseey tayi "mum Nasha ganinsu tare, sai inganta ta firgita shikuwa yayita murmushi, nifa gani nakeyi kamar daɗi yakeji idan yana bata tsoron. "Oh shikuma Aayaan irin tashi soyayyar kenan, Lallai Amma Allah ya zaɓa mana Abinda yafi Alkhairi....... Mummy tace tana gyara zaman muhsien wanda tuni yayi barci a cinyarta... Ƙarar shigowar kiran mijin Aseey ne a waya yasa mum yin shiru ita kuma Aseey ta ɗaga fuskarta cike da murmushi..... ° Aayann nanan yanata faman neman hanyar dazai tsokani Nawaz amma Sam taƙi biye mishi, Murmushi ya saki sakamakon wani abu daya tuna. Gyaran murya yayi "sister nifa ban yarda cewa sarfraz ba saurayinki bane, duba da abubuwa da yawa, bayan nan kuma da Yadda kika damu dashi. Wata lukutar harara ta zabga mai "me kake nufi? Nifa naga ka damu da zancen sarfraz ne, ina ruwanka dashi? Kuma ko da shi ɗin saurayinki ne meye ruwanka? Hamdala Aayaan yayi azuciyar shi, shi dama so yake suyitayi, sai gashi cikin sauki Allah ya kawo mishi mafita. Niko nakeda ruwa kuwa, sannan inason nayi investigation ne akan shi,. Domin Ni sam banma yarda dashiba, ya za'a ayi ace ba'a ga mutum ba sam... Ran Nawaz ne ya ɓaci "kanaji Ni babu ruwana idan munje can gidan nasu sai kayiwa iyayenshi bayani, pls kabarni da iya fargabaar da take damuna. "Fargaban me kikeyi? Hawayen da taketa riƙewane suka zubo a saman kumatun ta "babu ruwanka dani" "Haba sister daga tambaya? Nifa banyi haka don in ɓata Miki Raiba, pls i am sorry kibar kukan.. beso kukan nata ba shi yayi hakane don ya tsokaneta tayi magana Kara fashewa da kuka Nawaz tayi "nifa tsoro nakeyi kada Mummyn sarfraz tace Ni na batar mata da yaro, kuma Ni bansan ta yadda zan iya shiga gidansuba. Aayann ya fahimceta sosai kuma yasan tabbas ko shine haka ta faru saiyaji fargaba bare Nawaz daya lura tanada sanyin hali "ki kwantar da hankalinki, Insha Allah babu abinda zai faru zanyi Mata bayani kinji. Gyaɗa kai Nawaz tayi, Hannu yasa a aljihu ya ciro wani farin hankie me kyau sai kamshi yakeyi " amsa wannan maza ki goge hawayen cry cry. Amsa tayi tana rufe fuska dashi... Sai motar tayi shiru kowa da abinda yake tunani.... Sai wajen ƙarfe daya suka isa Kano, driver's ɗin ne sukayi parking saboda ganin lokacin sallah yayi, kuma sunsan oga Aayaan baya wasa da Sallah.... Wani store ɗin Rufaidah yogurt Aayaan ya shiga ya kwaso musu yoghurt dasu ice cream.... Su kuma su mummy suna cikin Masallacin dake gefen store ɗin duk sunyi Alwala suna jira Aayaan yazo ya jasu sallah, dayake an riga an idar a masallacin.. NAWAZ tayi mamakin yadda taga Aayaan yana Sallah cike da kwarewa, domin ya bata hakkin ta, daga farillanta har sunnoninta... Hakan yasa takeson taji cikakken tarihin wannan ahalin. Mummy ke ce mata "Nawaz kika gujemu, maimakon ki zauna muyi hira shine kika gudu donma Aayaan yaƙi yayi tukin wai zai tayaki zama. Murmushi Nawaz tayi "Mummy babu komai banaso nasa ku matsu ne . "To shikenan Nawaz babu komai. Nan suka zauna sukaci snacks ɗin da nawaz ta hada musu sukayi toping da yoghurt ɗin da Aayaan ya siyo musu. Ɓangaren Nawaz kuma kasa ci tayi sai ice cream ɗin tasha Duk yadda mummy ta matsa mata akan taci cewa tayi ta ƙoshi. Haka suka koma cikin motar kamar yadda suke da, shiru Nawaz tayi bugun zuciyarta na ƙara gudu, duk fargaba ta kamata.. Tsaff Aayaan ya lura da halin da take ciki amma besan yanda zaiyi mata ta saki jikinta ba.. Wata dabara ce ta faɗo mishi ya ɗago daga kishingidar da yayi ya gyara zama sannan yace "sister Saudiyya nakeso inje, zaki biya min? Duk da tashin hankalin da Nawaz take ciki hakan be hanata yin guntun murmushi ba "nikam yaya Aayaann ina naga kuɗin dazan kaika makkah? Daɗi Aayaan yaji ganin murmushi shimfiɗe a fuskar Nawaz, ya rasa meye alaƙar shi da ita da yasa sam bayaso ya ganta cikin damuwa... Murmusawa shima yayi "kefa yanzu billionaire ce, kinsan fa president da kanshi yake neman ki, ga Governor da Minister's, kefa yanzu shugaba ce take Miki baya Yakamata nariƙayi.. Murmushi kawai takeyi tama kasa cewa komai, Chan kuma ta numfasa tace " Ni awa? pls ka rufa min asiri babu ruwana, kuma naga kai har harbinka akayi a hannu amma kaƙi faɗawa kowa.... Kuma duk ta sanadi na, sannan Ni babu abinda nake bukata agurinsu duka don banaso a baza fuskata a duniya, "Meyasa" Aayaan yace a takaice "Saboda tsaro mana, kuma babban reason Dina ma shine kada fuskata ta zama unvaluable kowa ya Sanni, gaskiya hakan zaimini ciwo idan akace duk kafar sadarwa da jaridu akwai photona... Saida Aayaan ya tafa mata, saboda yadda ta nuna kishin kanta ƙarara, kuma yaji daɗin yanda tasan ciwon kanta.... A haka yaketa janta da hira, sosai yayi ƙoƙari ya cire mata damuwar da take ciki. A cikin hirar da sukeyi ma ya ɗan tsinci abu masu yawa daga cikin rayuwar ta, hakan kuma yasa ta ƙara shiga ranshi sosai, Ganin anzo kwangila fly over yasa Nawaz tace idan drivern ya sauka ƙasa zamu bar babban titi mubi cikin gari... Magana Aayaan yayi wa drivern, cikin girmamawa ya amsa yanayin ƙasan gadar a hankali . Ta cikin G.R.A sukabi sannan suka fito tacikin anguwarsu wato gaskiya layout, Aayaan kanshi daya saba da ganin gidajen alfarma amma Saida unguwar ta burgeshi saboda anyi gine-ginen ne cikin kwarewa da tsari, gasu madaidaita. Dai dai Kofar gate ɗin su SARFRAZ Nawaz tace "Anan za'a tsaya. Parking ɗin motocin duka sukayi sannan kowa ya fito. Tsaye Nawaz take ta kasa shiga gidan, zuciyarta sai bugun tara tara takeyi... Mummy ce ta matsa kusa da ita tace "my daughter be strong, we are with u, all will be fine Insha Allah. Aseey ta kalla taga ta ɗaga mata kai alamun eh, shima Aayaan ɗaga mata kan yayi haɗe da yimata murmushi... Tana nufar gate ɗin ya zuge da kanshi, a tare suka shiga cikin amma banda securities ɗin Aayaan.. Saida suka ɗanyi tafiya sannan suka ƙarasa ƙofar main falour ɗin Alarm Nawaz ta dannan ba'a daɗe ba saiga mummy ta bude kofar, wata irin ƙara ta saki haɗe da rungume Nawaz tana janta Cikin faloun " Alhaji dama na faɗa maka SARFRAZ ɗina be mutu ba, kaga Nawaz!!! Tausayin mum ne duka ya kamasu, cikin sanyin jiki suka bi bayan mumy zuwa cikin faloun... Nan kuma shima daddyn sarfraz ne yaketa nuna mummyn Aayaan jikinshi na rawa... Kowa tsayawa yayi yai turus yana kallon ikon Allah Zubewa daddy yayi a kasa warwas. Cikin tashin hankali duka sukayi kanshi aguje... Nawaz ce tayi karfin halin ƙarasa wa kitchen ta ɗebo ruwa.. Da sauri Aayaan ya amshi ruwan ya fara yayyafawa Daddy yana Tofa mishi addu'oi.. Wata irin nannauyar ajiyar zuciya daddy ya sauke sannan ya fara buɗe idon shi a hankali, da sauri ya maida idon ya rufe Sakamakon fuskar mummyn Aayaan daya gani. Gyara mishi zama Aayaan yayi Amma zuciyarshi cike take fam da tambayoyi da damuwa kala kala.. Mummyn sarfraz ma haka domin sam bata fahimci Abinda ke faruwa ba... Sai bayan Kowa ya natsu Mummyn Aayaan ta gaishe da mummyn sarfraz tare da gabatar da kansu a matsayin yan uwan Nawaz, da kuma yiwa Mummyn sarfraz ɗin Allah ya kyauta akan abinda ya faru, Anan ta sanar mata suma babu yanda basuyiba akan neman sarfraz ɗin Amma basu ganshiba..... Murmushin da yafi kuka ciwo mummyn sarfraz tayi "Ni inaji a jikina sarfraz yana raye kuma Insha Allah, Allah zai bayyana mana shi. Tare duka sukace "Allah yasa hakane Ameen. Allah ya bayyana shi. Kuma Gaskiya tunda Allah ya nunamin Nawaz naji Kashi 40 daga cikin damuwata ta ragu... Daddy yana nan zaune inda yake bece ƙala Ba, kuma be buɗe Ido ba. Aayann ne yacewa Mummyn sarfraz "mummy don Allah kiyi wa Daddy magana akan ya taimaka ya bude idonshi ya kallemu, bamusan me mukayiba, muna rokon afuwa... Gabanshi ta karasa tana yi mishi Magana ƙasa ƙasa, da kyar Daddy ya iya buɗe baki yace "kareemah waccan matar da kike gani itace maman sarfraz pah... Jin maganar da Daddy ya faɗa yasa kallon kowa ya dawo kan mummyn Aayaan, itama kanta take kallo, sannan Daga bisani tace "A'a wallahi banida Wani ɗa daban, yarana uku kuma daya ya rasu sannan Shima ba sunanshi sarfraz ba... Itakam Nawaz miƙewa tayi"wai wane sarfraz ake magana ne? °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° SARFRAZ bawan Allah anacan ana rikici a kanshi shiko yana nan baima san a wace duniyar yakeba, marabarshi da gawa numfashi da yakeyi.... Yauma kamar kullum hassu ce gefenshi ta zauna tayi jugum tanata kallon yatsun hannunshi, wanda daga bisani takai hannunta ta riƙe, addu'a taketayi idonta na zubda hawaye, Bandi beje kawoba yau saboda yanaso yaje can kauyen gabansu dan ya nemowa sarfraz maganin dazai wanke mishi ciki kila su samu yayi bayan gida... Hassu ce ta fito da gudu daga cikin bukkar still tana nuna mishi cikin bukkar tana ihu.. A rude bandi yace "hassu menene yasameta? Ta... Taa... *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ🎀🎀* *Episode 34* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu*✍️ "Ta motsa hannun ta kuma ta ƙifta ido" abinda hassu ta iya faɗa kenan Sannan ta kama hannun bandi tana janshi. Binta ya riƙa yi kamar igiya har cikin bukkar, Mamakine sosai ya kama bandi ganin SARFRAZ yana yunƙurin tashi daga kwancen dayake, kasawa yayi saboda ciwon dake kirjinshi ga kuma tsami da jikinshi yayi Saboda daɗewa da yayi a kwance na ƴan kwanaki ... Da sauri bandi ya rikoshi yana gyara mishi zama, itako hassu sai faman tallan MacLean takeyi. "Sannu kinji" bandi yace yana zama kusa dashi Yatsina fuska SARFRAZ yayi Yana yiwa bandi kallon rashin sani. Ki kwantar da hankalinki zamu faɗa miki ya akayi kikazo nan. Yatsina fuska SARFRAZ ya kumayi "i want to poo" Kasan cewar bandi yadanyi karatu yasa ya gane i want Yana nufin ina son,, da sauri yacewa sarfraz ɗin "mekiso" domin shi sam baisan me poo yake nufiba.. Miƙewa yayi ya fara mammatse ƙafafuwan shi Yana Daɗa cewa i want to poo. Hassu ce tace "bandi kasan fa ta daɗe batayi bayan gidaba koshi take nufin zatayi? Ai da sauri bandi ya riƙe shi muje, ƴar guntuwar bukkar da suke zagayawa ya kai sarfraz yace to shiga kiyi anan.. Kwalalo ido sarfraz yayi waje "Wallahi Ni ban iya Anan ba, shiru bandi yayi Yana tunanin ta ina zai fara.. "Kiyi hakuri kiyi bayan gidan anan bansan inda zan kaiki kiyi ba, Tsalle sarfraz ya fara yana cewa wayyo mummy ya matseni! Duk bandi ya ruɗe "ki shiga kiyi don Allah akwai maganar da nakeso muyi. Zuwa gaban bandi yayi yace " to cire min wandon. Zip ɗin babban wandon ya zage mishi sannan ya cire mishi ya barshi da karamin boxers ɗin, shidai bandi mamakine ya kasheshi yanaso yayi tunanin meyasa sarfraz yakeyi abuu irin na ƙananan yara amma kwakwalwar sa ta kasa saboda cunkushewar da tayi da mamaki. Yana kallo sarfraz ya shiga Cikin bayin da kyar yana gunguni, guri ya samu a gefe ya zauna yana jimamin Wannan al'amari... Ba'a fi minti Shida da shigar sarfraz bayin ba ya fara cewa "Nagama" Kasaƙe bandi yayi yana mamakin wannan wane irin abuu ne, ko dama su haka yan Birnin sukene, komai sai anyi musu... Ruwa bandi ya ɗebo a ƙaramar gora ya mika mishi "gashi ka wanke" Ihu sarfraz yasa akan cewa shi sai dai bandi ya wanke mishi, nanma ansha fama kafin SARFRAZ ya yarda ya wanke da kanshi sannan ya fito daga bayin yana hararar bandi "Babu ruwana dakai, kuma bazan sammaka biscuit dinaba idan daddy ya siyomin" Mutuwar tsaye bandi yayi yana kallon sarfraz. "Anya meye wannan takeyi hakane? Bin sarfraz yayi a baya. Shikam sarfraz na karasawa ya tarar da hassu zaune tayi tagumi, ƙarasawa gurinta yayi "aike zan san miki biscuits ɗina amma bazamu ba wancan ba ko? Yana nuna bandi... Murmushi hassu tayi tace "to" dukda cewa ita bawai ta gane me yake nufi bane ... Wuce su bandi yayi Ya shiga ɗaki, be ko kallesuba Saboda shi kadai yasan me yakeji, a zahiri idan ka kalli bandi zaka iya cewa su yan biyune shida hassu kasancewar yanada ƙaramin jiki, amma a baɗini shekararshi goma sha takwas, koda yake basaina zauna yi muku bayaniba kunsan dai yadda jikin Ƴan Fulani yake. Fitowa yayi rike da mayafin hassu "amshi kasa hassu, zamuje gidan baba jauro ne yanzu... Aikan dai shima SARFRAZ saiya fara kici-kicin maida wandonshi yana cewa Nima zani "irin dai yanda yara suke yi.. Amsar wandon bandi yayi yasa mishi sannan suka nausa cikin daji... Duk Abinda sarfraz ya gani a hanya saiyace meye wannan, idan na taɓawa ne ya taba.. A haka dai a lalace suka karasa gidan baba jauro ɗin, duk sun gaji kasancewar Akwai tazara sosai tsakanin su... A cikin bukkar shi suka taddashi zaune ya rungume allo yana rubutun ajami ajiki. Yana ganinsu ya fara murmushi ya ajiye Allon a gefe, "maraba da Aliyu da hafsatou... Suma murmushin sukeyi sannan suka samu guri suka zauna, Gaisheshi sukayi cike da mutuntawa, shima a sake ya amsa musu yana murmushi... "Yau kuma ziyara akan kawo mana? "Eh baffa" cewar bandi Yana Dada gyara zama.. Kallon sarfraz baba jauro yayi sannan yacewa bandi "baƙo mukayi ne? Eh baffa a hanya muka tsinceta rannan, nan dai bandi ya faɗawa baffan duka Abinda Ya faru tun randa suka tsinci Sarfraz har zuwa yau daya farka da kuma abinda yayi bayan ya farka.... To dayake baffan yayi zaman Maraya sosai, ya zauna a Kano, ya zauna a Abuja har a Lagos ma ya zauna, to hakan saiyasa ya fita daban cikin rugar saboda yanada wayewa sosai sama dasu.... Ashsha! Allah dai yasa ba Abinda nake hasashe bane ya faru.... Cewar baffa yana miƙewa. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Gyara zama mummy tayi tace SARFRAZ dai da kika sani. "A'a To naji anacewa Ammah ce mamanshi, to kefa? Nawaz tace tana daɗa maida hankalinta gaba ɗaya gurin mummy. Murmushin ƙarfin hali mummy tayi " ai dama tun usuli banice haƙiƙanin Wadda ta haifi sarfraz ba, amma koshi kanshi besan da hakaba... Mummyn Aayaan ce tayi gyaran murya sannan tace "Don Allah inaso hankalin kowa ya dawo gareni.. Farko dai Ni sunana mehtab mu yan biyune nida ƴar uwata mumtaz.... Ayanda mariƙai na suka bani labari shine ance wai a tsincemune a Kofar babban masallacin juma'a dake Faisalabad a ƙasar Pakistan... To shine aka kaimu gidan marayu, anan muka girma nida Yar uwata mumtaz komai tare mukeyi gashi Allah ya ɗora mana wata irin ƙaunar junammu, banaso wani Abu ya samu dayanmu koda wasa.... A haka mukayita girma har mukakai kusan shekara goma, Wata rana wasu mutane mazauna Pakistan amma asalin su yan Sudan ne aikine ya kawosu Pakistan.. Suka zo gidan marayinmu suka cike Form akan zasuyi adopting dina, to duk cikinmu babu wanda baisan irin kaunar da mukewa junanmu ba.. Haka akace wa mumtaz tabi yayinmu zasu kasuwa, Ni kuma bayan sun tafi waɗan nan mutane suka tafi dani. Na daɗe ina ciwo, nayi kuka nayi kuka har na gaji, sai dai kawai su bani hakuri, daga bayane suka bani wannan zoben sukace in ajiye shi a hannuna idan na girma zasu kaini gurinta, wai itama sun bada irin wannan zoben a bata.... To haka dai na hakura inata rayuwa amma sai dai zoben nan ya zame mini kamar mumtaz haka zàn Zauna Ni kadai inyita magana da zoben ina murmushi.. Kuma kullum fatana baya wuce Allah ya kawo Ranar da zamu haɗu da yar uwata... To dayake garin da muke anayiwa yara aure da wuri to saiya zamana banfi shekara sha uku ba maza sukayi ta tururuwa akan suna sunason aurena... Babana yaƙi yarda sam saboda yasan bazasu rikeni Yadda ya kamata ba. To anan ne daga baya Allah ya haɗamu da babansu Aayaan wani lokaci da akayi rikici a Sudan , to yana daga cikin waɗanda suka zo bada tallafin gaggawa a jirgin sama, da kuma tallafawa ga wadanda iftila'in ya faru dasu..... Kwarai mariƙa na sunyi amanna dashi suka bashi izinin ya rika zuwa lokaci bayan lokaci.. To sanda nakai Shekara Goma sha biyar sai aka daura mana aure akayi abubuwan da aka saba na al'ada.... Mun shaku sosai da mijina, saboda baya boyemin komai kuma yana matukar kyautata mun yana kaunata sosai.. Anan Sudan ɗin muka zauna na tsawon lokaci saboda hatta Aayaan Saida yakai shekara 15 tukuna mijina ya Nemi transfer akan zai koma ƙasar iyayenshi. Munyi kuka sosai sosai nida marikana, haka muka dawo Nigeria, to dayake mijina yasan da mumtaz tun kafin muyi aure. Bamu Dade a Nigeria ba yayi mana visa zuwa Pakistan don ya cika min burina naganin yar uwata. To Abin baƙin ciki shine koda mukaje sai akace tayi aure wai tabi wanda ta aura ma Nigeria amma zasu dawo, to saina ce abani address Dinsu na Nigeria saboda muje, amma sai sukace basuda shi, haka na ajiye musu numberta akan idan sun dawo a bata ace mata nazo amma bamu haduba. To tundaga wannan lokacin Allah bai kuma nunamin yar uwa ta ba, kullum da ita nake kwana nake tashi, duk sujadar da zanyi sainace Allah ya nunamin yar uwa ta.. To cikin ikon Allah kuma sai ya Turo mana da Nawaz a lokacin da bamuyi tsammaniba. Kuma hakan yasa ..... Gashi dai ba don halinkuba, amma gobe idan adadin liking ɗin bekai yadda nake soba zakuji wayan ne,👀👀 *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *Episode 35* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Kuma hakan yanada nasaba daga zoben dana gani a hannunta, to bayan nayi mata bayanin zoben shine tace min itama ba nata bane wai Sarfraz ne ya bata, To yanzu mudai munzone a dubemu da idon rahma akan zoben nan don girman Allah idan kunsan wani abu akan shi ku faɗa min. Daddy wanda tunda ta fara magana yake tuna yadda mumtaz take nuna mishi muhimmancin zoben sanda tana raye, har randa zata mutu Saida ta bashi zoben a matsayin amana idan SARFRAZ ya girma ya bashi. Ashe shi SARFRAZ ɗin ma yaje yayi kyauta dashi, mummy kuwa harda kwalla domin tasan labarin zoben kuma tasan idan mehtab taji mumtaz ta mutu akwai damuwa duba da yadda ra kwallafa ranta akan ita Yar uwar Tata. Gyaran murya daddy yayi haɗe da gyara zamanshi sannan yace "tabbas babu ko tababa duk Wanda ya ganki yaga ƴar uwarki mumtaz, kamar takuma har ta ɓaci domin Ni dana gankima sam na manta cewa tace ku Yan biyune, nayi zaton ko fatalwace... Sai daga baya na tuna, yanzu abinda nakeso dake shine kinsan komai na duniya Allah ne ya halicce shi, kuma sanda zai halicce shi beyi shawara da kowa ba, kuma babu wanda ya tayashi yin halitta. Kinga kuwa duk abinda yayi dai-dai ne, sannan kuma babu wanda ya isa yace yafi Allah son halittar shi. Rayuwa da mutuwa kuma duk suna gurin Allah, babu wanda yasan Sanda zai mutu, zai kai gobe balle jibi. Kuma Allah yanason masu hakuri, kuma yanason waɗanda idan kaddara ta samesu ko wace iri ce su amsheta hannu biyu . Mummyn Aayaan ce ta katse shi dacewa "komenene kafaɗa min kada kaji komai, Ni dama tuni zuciya ta ta hakura da koma me zanji, amma ina so nasani tabar wani abu dazan riga ganinta dashi? Kowa na ɗakin idonshi cike yake da hawaye, shikuwa daddy mamakin irin ƙarfin imanin mehtab yakeyi. Ayanda ta nuna ƙaunar ƴar uwarta be tava tunanin zata amshi ƙaddara haka da wuri ba. Daddy ne ya fara magana a nutse " nine mijin mumtaz, mun haɗu a University of pesherwar Dake Pakistan , daga baya mukayi aure....... Nan dai Daddy ya gama bata labarin har zuwa inda bayan ta haihu Allah ya amshi ranta, Mummyn Aayaan tayi kuka sosai sai dai na zuci, domin idan ka kalleta hawayene Kawai ke zuba a fuskarta baya ko tsayawa.... Babu wanda beyi kukanba, sannan kuma kima da darajar mummy ta Karu a idon kowa dake falon saboda sunji yadda ta rike sarfraz babu kyara babu tsana bare tsangwama... Haka dai akayita jajanta wa juna, haɗe da alhinin abubuwa da yawa da suka faru... Nawaz na gefe babu abinda ke fita daga idonta sai ruwan hawaye, tayi iya kokarinta akan ta tsaida shi Amma ta kasa .. Mamakin halin Mummy takeyi, irin yanda take nunawa SARFRAZ ƙauna babu wanda bazai dafa Kur'ani yace itace mamar shiba... Lallai ashe har Yanzu Akwai masu yin soyayya don Allah... Duk motsinta idon Aayaan na kanta dukda shima yana cikin damuwa amma ganinta da yayi a hakan saiya kasa sukuni, bini bini idonshi na kanta.... Rarrafowa Nawaz tayi zuwa tsakiyar falourn sannan ta tsuguna ta haɗa hannayenta guri guda tana rusa ihu, muryarta har rawa take yi tsabar damuwar da take ciki ga idonta ya kumbura yayi jajir. "Don Allah ku yafemin, wallahi ba'a son raina muka rabu da sarfraz ba, babu yanda na iya ne shiyasa... Amma nayi muku alkawarin hardai yana raye saina nemo muku shi, dukda Nasan bazaku Dena kallona a matsayin wadda na jawo muku bakin ciki da cikas a rayuwaba amma ina rikon alfarma akan kuyafemin idan zaku iya .. Mamakine ya kama kowa a falour, domin sam basu lura cewa Nawaz kuka taketayi ba Saida ta fito tsakiyar faloun. A Tare mummy da mummyn Aayaan suka mike suka kamata "haba ke kuwa Nawaz? Meye haka? Ji yanda kike kuka, So kike ciwo ya kamaki, to gaskiya idon kinason zaman lafiya ki cire komai a ranki kiyi sabgarki kamar yadda kikaga muma munayi.. Sannan kuma ki Dena tunanin cewa muna kallonki da wani abu, Wallahi sam ko ɗaya illah ma Barka mukeyi da duka baku halaka ba. Kuma gashi ta dalillinki ma an kuma haɗa zumunci da bakinshi ya wargaje.... Shima daddy cewa yayi "Nawaz Yar albarka, yanzu idan sarfraz ya dawo Kinga saimu fada mishi mahaifiyar shi ta rasu saboda ya rika yi mata addu'a, kuma duk kece sanadi, saboda da na kasa fada mishi ne saboda bansan suwa zan nuna mishi a Matsayin yan uwanshiba. To Kinga yanzu kin kawo mini su har gida... Ɗago kai Nawaz tayi "Daddy dagaske sarfraz zai dawo? Daga mata kai yayi yana murmushi "zai dawo insha Allah, kidena damun kanki kinji, addu'a kawai ya kamata kirika yi akan Allah ya bayyana shi.... Hakanan Aayaan yaji zuciyarshi nayi mishi suya, dukda yanzun nan yasan Cewa sarfraz kaninshine amma idan yaga Nawaz tana nuna damuwa akan shi saiyaji kamar zuciyarshi zata fashe... Ya kasa fahimtar wannan wane irin al'amari ne me rikitarwa, meyasa zai damu? Inaruwanshi ma? Haka dai ya daure zuciyarshi yaci gaba da kallonsu. Tashi kowa yayi donyin Sallah inda mummy ta nunawa Aayaan ɗakin SARFRAZ tace ya shiga chan, su kuma suka tafi dakinta tare... Duk Nawaz ta kasa sakin jikinta, kome zatayi a ɗarare takeyi domin jinta kawai takeyi kamar mujiya a cikin tsuntsaye... Duk su Mummy sun lura da hakan, barinma aseey wadda sai janta takeyi da hira saboda Ta saki jikinta... Koda Nawaz ta idar da Sallah samun guri tayi a daddumar ta jingina da jikin gado tanata azkhar saboda an kusa kiran magriba domin basuyi sallar da wiriba saboda zaman da sukayi . Duk abinda take yi Aseey na lura da ita, duk sai takejin babu daɗi sam... Kowa yasan ƙaddara ce, kuma dole dama hakan saiya faru tunda Allah ya riga ya tsara Hakan tun tuni . Tashi tayi ta fita zuwa falour, dakin sarfraz ta shiga Domin tanaso suyi magana ita da Aayaan.. Cikin Sa'a kuwa ta tarar dashi a zaune a saman gado yana kallon photo album ɗin sarfraz... Zama tayi suka kalla tare, abin gwanin ban tausayi domin Saboda sarfraz kaman zaiyi magana... Tabbas kuma sun tabbatar sarfraz ɗan uwan sune, domin babu waybda zai kalli hoton sarfraz kuma ya kalli Aayaan be rantse cewa kaninshi bane harta da hancinsu iri dayane da yanayin gyaran gashinsu da saje, saidai sarfraz yafi Aayaan fari Kasancewar shi farin mahaifiyar shi ya dauko sukuma su Aayaann Golden skin Ɗin babansu suka dauko. Gyara photon Aayaan yayi ya maidasu inda suke "sis Wallahi inaso naga SARFRAZ, kuma Insha Allah saiya zama soja har dai yana raye. Nine kullum dama cikin yin korafin Ni Banda kani to ashe Allah ya bani ban saniba... Murmushi Aseey tayi "Allah dai ya Bayyana mana shi, Nima wallahi ina son naganshi.... "Hmmm sis ƴan uwa daɗi garesu, yau kawai da mukaji gaskiyar lamarin yar uwar mummy duk mun samu salama a ruhinmu. Kuma yanzu mun ƙara yawa ko babu komai zamu bigi kirji mu nuna daddy muce dan uwan mummyn mune, wanda ada bazamu iya ba. Murmushi Aseey tayi "Maganar ka gaskiya ce, Allah ya kara datar damu. "Ameen " Aayaan yace yana mikewa "Koma ka Zauna inaso muyi Magana.... "Komawa yayi ya zauna yana Maida hankalinsa zuwa gareta... ""Aayann inason muyi Magana ne akan Nawaz. Ɗago kai Aayaan yayi ya kalleta. "Ko kaine a matsayin da Nawaz take yanzu dole saika rikayin abinda take yi , saboda she is feeling guilty of her self, Gani take itace sila, so yanzu ina sone mu hada kanmu Wajen Bata farinciki... Bazai yiwu mu rabota Daga Wajen iyayenta ba mu kuma ta riƙa chutuwa ta sanadin muba. "To sis yanzu me kikeso ayi? "Yauwa my bro, inasone anjima bayan anyi sallar isha'i ku fita tare kaɗan kaita guraren maybe taɗanji sauki, amma fa ba wai ƙiri ƙiri zaka nuna mata ita zaka kaiba, zakacene muhsien zaka kai amma kai baka san guraren ba tazo ta raka ka. Murmushi Aayaan yayi, domin yaji daɗin wannan al'amarin "to sis Insha Allah..... Hirar sanda suna makaranta suka farayi har zuwa sanda aka kira magrib Sannan Aseey ta koma daki, shi kuma Aayaan ya shiga bathroom don ɗauro Alwala, sai murmushi yakeyi shi kadai. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° "Baffa meya faru da ita? Bandi yace tare da maida duka hankalinsu gurin baffa "Eto na lura da wani abuu kamar wannan saurayin ya kamu da ciwon mantau ne fah! Sarkewa Muryar bandi tayi har Saida ya ɗan yi tari tukuna yace "baffa kana nufin ciwon mantau ne ya kamashi? "Eh gaskiya abinda nake tunani kenan amma bari mugani. Gyara zama baffa yayi ya kallon sarfraz sannan yace "ɗan samari yaya sunan ka? Gab dashi sarfraz ya matso sai murmushi yakeyi "sunana sarfraz, "Yauwa to shekarar ka nawa? Shiru yayi yasa yatsanshi a baki alamun tunani sai daga baya kuma yace "bansaniba, na manta Amma idan naje gida zan tambayi mummy gobe saina faɗa muku... "Shikenan Wallahi ta tabbata, Sai dai nashi akwai sauki saboda bata ɗin din din bane, ana sa ran idan yaga wanda ya sani zai tuna komai Insha Allah... Kuma yanzu zai iya gyaruwa ma saboda kwakwalwar shi tazama kamar ta yara duk abinda kuka nuna mishi shi zaiyi kuma idan kukace ya dena zai dena... Hassu dake gefe tun ɗazu tana jin jawabi sai yanzu ta sako baki "baffa kana nufin wai yanzu mu kaɗai ya sani? "Tabbas a Yanzu kafin ya koma dai dai babu wanda ya sani irinku... Don haka nake rokon ku akan gobe ku kawo minshi satu mu kaishi asibiti aduba ko za'a iya yimishi wani abu, sannan wannan ciwon nashi a wankeshi a bashi magani dukda naga kayi kokari sosai ciwon yayi kyau be kwaɓe ba.... Sallama sukayi da malam suka shiga ciki suka gaida adda balki sannan suka fito sukayi hanyar gida ..... Garin yai duhu saboda magriba tayi hakan yasa sarfraz sai wani shigemusu yakeyi alamar tsoro, gashi duk yayi biyinsu a girman jiki, Aikuwa da hassu da bandi sun gane me yake nufi Kawai sai suka mamaye shi suka kwasa a guje .... Ganin suna gudu shima ya kwasa ya bisu a guje yana ihu " wayyo Allah na wayyooo kujirani tsoro nakeji..... Irin dai yanda yara sukeyi a duhu..... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Kowa na zaune a falour amma banda Nawaz domin har yanzu ta kasa sakin jikinta, koda tayi sallar isha'i sai kawai tayi wanka ta nemi guri ta zauna tayi jugum, babu abinda keyi mata yawo a zuciya face fuskar SARFRAZ sanda yake yi mata shakiyancinsa.... Sanda zasu fita falour Mummy tayi tayi da Ita akan ta fito amma sai tace suje tana zuwa... Achan falourn Aayann ne ya fito sanye da kuftan farare ɗinkin ya amshi jikinshi tsaf Gashi ya ɗora hula baƙi da ratsin fara, sai yayi wani sharr dashi Kamar ka saceshi ka gudu.... Zama yayi yana tunanin yanda zai kira Nawaz ganin babu ita a falourn.. Aikuwa be gama gyara zamanba muhsien yayo kanshi da gudu yana cewa "Uncle please muje ka kaini wajen shan ice cream... Wani irin daɗi Aayaan yaji ganin abin yazo mishi cikin sauki.. Amma sai yace wa muhsien ɗin sorry ka bari sai gobe sai muje Koh? Ai nan fa ake yinta muhsien dagewa yayi ya fara ihu yana cewa "Wallahi kuma babu ruwana dakai, kuma mun ɓata kada ka kumamin magana... Nan hankalin kowa ya dawo kansu, Mummyn sarfraz ce tace "bazai yiwu ba maza ka tashi ka kaishi inba hakaba duk mu ɓata dakai, yazaayi ka ɓatawa mijin mu rai... "Mummy ai bansan gurinba kin manta mu baki ne? Duk Neman baasin da kakeyi don karkaje saika ce, Aseey jeki kira Nawaz kice ta tawo da mayafinta, ita saita raka ka ... Shi dai Aayaan sai murmushi yakeyi be taɓa tunanin abin zaizo minshi da sauki hakaba... Koda Nawaz ta fito jikinta duk babu kwari , fuskarta tayi fayau da ita alamun tana cikin damuwa. Mummy ce tace mata "my daughter don Allah ki taimaka ki raka su muhsien Apple white ko chicken republic, oh koma dai inane wai zesha ice cream ne.. Gaban Nawaz ne ya yanke ya fadi jin tare da Aayaan zasu fita, tana kallonshi tunda ta fito yake kallonta ga turarenshi dake damunta duk ya cika mata hanci... Mikewa Aayaan yayi yai waje domin yaga alamar idan ya zauna Nawaz zata iya rusa minshi lissafi. Kamar ta rusa ihu haka tayi musu sallama ta fita... A cikin mota ta tatar dasu suna labari, bata kulasuba illah dai ta samu gefen me zaman banza ta zauna.. Shima be kula taba Kawai ya ja motar yayi hanyar fita, saboda dama tun sanda ya fito yayi magana da securities dinshi aka kada su biyo shi .. Saida ya fita bakin titi tukuna ya kalli Nawaz "ranki ya daɗe ina zamubi? Nuna mishi tayi da hannu batare data kalleshi ba, sanin halin datake ciki yasa Aayaan be matsa mataba ba sam... Sunzo wucewa ta PZ muhsien ya hango hotunan waya nanma wata rigimar ya dauka "Uncle pls ka siyan mini ipad kaga Mummy ta bata tawo min da nawa ba, pls uncle . Cewa yayi "to zan siyan maka bari muyi Parking, bayan yasamu guri yayi Parking ne ya Kalli Nawaz kema zo muje! Batace komaiba ta buɗe kofa ta fita, suma suka fita ta ɗaya kofar. A tare suka shiga cikin store ɗin.. Namfa me store ɗin ya fara turo musu wayoyi kala kala yana cewa "Alhaji asiyanma maman boy mekyau Wadda idan ta shiga cikin kawaye za'a gane kanaji da Ita.... Dummmm gaban Nawaz ya buga da ƙarfi, atare suka kalli juna sai Kuma tayi saurin kauda kai... Murmushi Aayaan yayi "Kamar kuwa kasan dama inaji da ita sosai, yanzu zaɓar mini wadda tafi ko wacce tsada a shagon nan saika sa mata sim card da memory sai kuma ka samomin babbar ipad itama me kyau.... Kirjin Nawaz ne ya fara dukan uku uku daya saba yi mata, duk saitaji tsayuwar ma ta isheta.... Wani matashi ne yazo shiga cikin store ɗin saiya kalli su Aayaann da muhsien sai kuma ya kalli Nawaz, murmushi yayi yace gaskiya Madam yaronki yanada kyau sosai, ko don saboda dake yayi kama ne? Kai kuma Alh, baka lura Madam bata da lafia bane shine ka fito da ita, Ƙasa ƙasa yayi da murya sai kuma yace "ko an samar wa da boy Kani ne ko kanwa? Ai fuuu Nawaz ta fita daga store ɗin tayi hanyar mota, tanajinsu sunayi mata dariya *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ🎀🎀* *Episode 36* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Koda ta shiga motar ta zauna abin bai fita a ranta ba, inbanda hauka daga ganin mace da namiji sai akace dole su zama mata da miji, babu tunanin yaya da ƙanwa. Tsaki ta kumayi "taya ma zan yarda na auri mutumin da nakejin tsoro da fargaba duk sanda ya tunkaroni? Wani irin ɓacin rai ne ya tunkarota, "gaba ɗaya yanzu ma naga kamar an maidani kamar kwallon tamola ne, daga wannan ya jefani chan sai wannan yayi chan Dani.. Kuma ummi ta zuba ido "tsaki ta kuma yi tana daɗa shiga Duniyar tunani, "duk sanda kaganka a cikin wata rayuwa to ka godewa Allah domin da za'a canza wani abuu ƙalilan a cikin rayuwar sai kaga komai ya jagwalgwale maka. Tunda nake a rayuwata ban taɓa tunanin akwai ranar da zansan gidansu SARFRAZ ba balle har inje cikin gidan nasu na kwana ba, sai gashi ƙaddara takaini har hidima sukaitayi dani, kuma dalili na yanzu babu sarfraz ɗin. Ba'a barni haka ba yanzu kuma na fada gidansu Aayaan, daga ayi nan sai ayi chan, still yanzu kuma ga wani sabon zance "taɓ wallahi ma bazai yuwuba, tiburewa kawai zanyi a maidani gurin ummina. Rayuwata tada tafi daɗi, da ace ana tambayar mutum kafin abu ya sameshi, to wallahi nidai da nace gwara abarni yanda nake ada koda kuwa su safraz ɗin zasu kasheni da tambayoyin rashin kunyar sune.. Acikin ƴan mintoci ƙalilan ta haɗawa kwakwalwar ta waɗannan tunanin... Zufar data tsatstsafo mata a goshi tasa gefen mayafinta ta goge. Buɗe ƙofar motar dataji za'a yi ne yasa ta daɗa murtuke fuskarta, don anata gani take inba haka tayiba to Aayann zai gama rainata ne, duba da dama ya rigada ya rainata ɗin. Zama Aayaan yayi a driver seat bayan ya zaunar da muhsien a back seat. Ganin Yadda Nawaz tayi kici-kicin da rai sai abin ya bashi dariya, amma baiyiba ya kanne. Gyararriyar ƙasumbar fuskarshi ya shafa yanajin wani irin feelings deep inside him. Be taɓa tunanin wannan zancen na mata da miji ba Sai yau tabbas wannan fitar tazo mishi da Alkhairi. A iya tunaninshi shidai yasan yanajin daɗi idan ya ganta sannan yana samun nutsuwa muddin suna cikin inuwa ɗaya, sannan yasan ko kaɗan bayaso ya buɗe ido yaga batanan duk saiyajishi incomplete... Kallonta yayi yana mamakin wai me take daurewa fuska hakane, sai kuma yayi murmushi mai sauti "maman boy meya faru naga kamar bakya cikin mood me kyau? Ɗaga Kai tayi ta kalleshi "sai mene don kace mini maman boy? Ai dama kowace mace uwace koda yau kuwa aka haife ta, balle kuma Ni da a ƙalla na wuce shekara ishirin, kuma dama ko baka faɗa ba muhsien ɗa nane tunda ɗan Aunty na ne.... Dariya abin ya bashi yanda ta dage tana sako mishi sharhi, "nifa ban faɗa don wani abuba kuma ba faɗa nake nema ba, i am sorry please 🙏 Dago da Kai tayi ta kalleshi charaf kuwa suka haɗa Ido, aiba shiri ta kauda kanta gefe sakamakon wani irin kwarjini da taga yayi mata fiye da kowane lokaci. Murmushi ya kumayi tare dayin igniting motar "ina fatan za'a nuna mana gurin ice cream ɗin? Duk sai ta nemi kwarin gwuiwarta ta rasa, tanaso tace bazata nunaba ya kaita gida amma Sam ta kasa sannan zuciyarta ta cika da fargaba... "Muje zan nuna" ta samu bakinta da furta haka. Shiru motar babu motsin kowa harta muhsien shima ya natsu, "nan ya isa! ga chicken republic ɗin chan, ka tsallaka ka siyo mishi ko kuma kayi Uturn saika shiga da motar. "Okay" kawai yace sannan yayi Uturn ɗin, parking ɗin motar yayi a harabar inda aka tanada don parking ɗin. "Madam muje" dum zuciyar Nawaz ta daɗa bugawa, Wannan kuma wane suna ya kuma nemowa? Amma saita basar "bazan shigaba" tace a takaice. "Inahh bazai yuwuba saikin shiga, kefa mayyar ice cream ce, Kinga sai ki zaɓi duk wanda kikeso tunda Kinga nibansan wane flavour kike soba... "A ina kasan Ni mayyar ice cream ce? Murmushi me Kamar dariya yayi "A hanyar Kano da muka tsaya lunch" Shiru tayi sai ta samu kanta da buɗe motar tana fita, shima fitowa yayi ya buɗe wa muhsien sannan ya ɗauke shi a kirjinshi. Hakan nan yau yake jinshi cikin wata Irin annashuwa... Nufar cikin gurin yayi yana takunshi na kasaita kuma ingarman namiji, wanda shi baima san yanayi ba, Nawaz na biye dashi kamar jela sai dai daka kalleta zaka gane jikinta a sanyaye yake.. Guri ya samu ya zaunar da muhsien sannan yaja mata kujera "ku zauna bari nazo" Kai kawai ta ɗaga mishi haɗe da zaunawa, muhsien ne yace "Aunty bakida Lafiya ne? Ɗan murmushi tayi mishi "eh muhsien, banajin daɗi ne! "Sorry Aunty! Idan Uncle ya dawo zansa siyo Miki magani. "No muhsien kabarshi naji sauki " Bece komaiba amma shima idan ka kalleshi zaka ganshi wani sukuku kamar bashida lafiya. Sunfi minti goma a gurin sai gashi ya dawo riƙe da manyan shopping bags niƙi niƙi, a gefe ya ajiye su sannan yace" na manta ban tambayeki wane flavours kikesoba. "No kada ka damu inashan ko wanne ma. Lura da yayi da yanayinta sai kawai ya kyaleta bece komaiba. Koma wa yayi ya kuma kwaso wasu ledojin harda staff Guda ɗaya shima riƙe da wata babbar leda..... Suna zuwa dai dai su yace "kuzo mu tafi" Mikewa Nawaz tayi da nufin zata kwashi ledojin daya fara kawowa. "Kada ki kuskura ki dauka, kinsan fa bakyida lafiya kawai ki tawo zan dawo na dauka . Hakanan duk saitaji wani iri, gaskiya ita bata saba da haka ba taga mutum yana aiki ta kasa tayashi balle wanda ya girme ta, Komawa tayi ta zauna . Staff ɗinne ya dawo yana yi mata murmushi "Madam gaskiya mijinki yana sonki sosai, Allah ya kara muku danƙon soyayyah, yace kitawo ku tafi zan dauki sauran kayan nakai motar. Ƙala bata ce mishi ba ta mike riƙe da hannun muhsien ta nufi hanyar kofar fita, don ita ta tabbata cewa kaddara ce yau ta fito da ita da daren nan ake ta ce mata matar Aayaan.... Koda ta fita direct Parking space ta karasa, a tsaye ta ganshi kofar motar a buɗe. Tare da muhsien ta shiga ta ɗora shi a cinyarta. Rufe musu ƙofar yayi sannan ya buɗe booth don staff ɗin ya zuba kayan daya kwaso. Zagayawa yayi ya shiga driver side ya zauna, a hankali taji ya karantar addu'ar hawa mota sai kuma taga yayi igniting motar sun dau hanya.... Tafiyar kurame aketayi inda Nawaz taketa tunanin hanyar da zata bi ta koma gida cikin sauki, domin itafa Wannan asha Ruwan tsintsayen da akeyi da ita ya isheta don a yanzu ma gani takeyi itafa babu wata Abuja da zataje, sai dai duk abinda za'ayi ayi, sam ta gaji, tanaso ta zauna ta nutsu ko ta samu damar yin addu'oi masu yawa akan sarfraz. Ta ɓangaren Aayaan kuma tunanin yadda zai shawo kan Nawaz yakeyi ta yadda zasuyi tsabtatacciyar soyayyar da zata kaisu ga aure, domin tun daga sanda mutumin ɗazu yace mata naman boy zuwa yanzu ya tabbatar yana son hakan ta faru .. Muhsien ne yace Uncle baza muje Apple white ɗin bane? "Zamuje" Aayaan yace a takaice yana maida hankalinshi zuwa kan titi. "Gaskiya muhsien kayi hakuri kawai mu tafi gida gobe sai ya kaika, cewar Nawaz tana ɗan ɓata rai domin ta fara gajiya da yawon.... "To Aunty" cewar muhsien ba tare daya nuna wata damuwa ba. Tsaki Aayaan yayi haɗe dasa hannu a aljihu yana ciro waya, a cinyar Nawaz ya ɗora "ga taki na manta ne" sai kuma ya maida hannun daya aljihun ya ciro ipad ɗin muhsien yace "my boy ga taka" da sauri ya amsa yana dariya.. Ita kuma Nawaz saita haɗa girar sama data kasa nifa bance ka siyan mini wata waya ba domin banida bukatarta. A ɗan zafafe yace "ai dama bance ke kikace na siyan Miki ba, ra'ayin haka nayi sannan ko bakida bukatarta hakanan zakiyi Amfani da ita. Jin yadda muryarshi ke fita yasa babu shiri Nawaz ta dauki wayar sai kuma wata zuciyar tace mata Nawaz baki kyautaba, be kamata Mutum ya siyan Miki abuu haka me uban tsadaba kuma ki Gwasale shi ba, ko babu komai ai dama kinason ki koma gida, yanzu kin samu hanyar da zaki riƙa magana da umminki duk sanda kikaga dama har ki samu ta baki shawara. ɗan ɗago da kanta tayi ta kalleshi "Nagode sosai ya Aayaan" Mamakine ya kamashi domin be taɓa tunanin zata yi mishi godia ba duba da yadda ta gwasaleshi da fari. Murmushi ne ya kufce mishi, be kalletaba be kuma amsaba be. Haka suka isa gida bayan yayi Parking ya fito itama ta fita ta tsaya "ku shiga ciki mana" "Zamu tayaka kwasar kayan ne" "A'a bakyada lafiya so just get in kada ki wahalar da kanki, babu yadda ta iya haka ta kama hannun muhsien suka wuce ciki. A falour ta tarar dasu duka sunata hira da alamu har sun saba saboda duka basuda wuyar sabo. Suna ganinta suka fara murmushi "har kun dawo daughter, sannunku da zuwa, ina Aayaan ɗin Mummyn sarfraz ta tambayi muhsien "Yanzu zai shigo ya tsaya kwaso kayane.... Be ida rufe bakiba Aayaan ya shigo riƙe da ledoji niƙi niƙi, ko wane hannu leda huɗu, ko achan ɗinma abinda ya hanashi dauka saboda kada mutane su kalleshi amma shiba nauyi sukayi mishiba .. Aseey ce tace"soja mazan fama, soja marmari daga nesa! Yau kuma an tuna da filin daga kenan? Ita dai Nawaz abin be wani Bata mamakiba tunawa da tayi sanda ya ɗauketa a daji ya ruga da gudu, juyawa tayi ta nufi daki,. Muryar Mummyn sarfraz taji tace "daughter kizo mucigaba da hirar tare mana... Ɗan marairaice fuska tayi "wallahi mum zazzaɓi ne ya rufeni, kuma barci nakeji.. "Subhanallah, sannu duka suka haɗa baki wajen faɗa.. Da ido Aayaan ya bita domin yasan saboda shine ta gudu hakanan saiya tsinci kanshi da rashin jin dadin tafiyar Tata "to ice cream ɗinki fa" yace yana nufarta da babbar leda guda ɗaya. Ai da sauri ta shige ɗakin don batason ya cin mata da wannan mayen turaren nashi dukda yau ta shaƙeshi har Saida ya cika mata ciki...... Ƙofar dakin ya tura ya shiga, firgigit tayi saboda batayi tunanin zai shigo ba, ai bata jira komaiba ta buɗe bayi ta shige da gudu ta rufe tana sauke ajiyar zuciya ..... Ledar ya ajiye a gefe yana murmushi, Ni na zama dodo kenan! Harɗe hannu yayi haɗe da fita daga ɗakin yana ganin zallar yarintar Nawaz °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Misalin ƙarfe bakwai da rabi ya safiya SARFRAZ ne zaune ya kasa ya tsare akan wai dole sai hassu tayi mishi wanka, bandi yayi yayi akan ya hakura shi zaiyi mishi amma Sam yace shifa na hassu yakeso tunda itace ƙawarshi, wai yana fushi da bandi saboda jiya yaƙi wanke mishi poo da yayi... Duk wata dabarar duniya hassu da bandi sunyi amma yaƙi yarda, shifa ala dole sai anyi mishi wanka kuma babu wanda zaiyi mishi face hassu... Da abin yaci tura sai sarfraz kawai ya fara rusa ihu baji ba gani.... Lallashin duniya amma yaƙi yin shiru, shifa a mishi wanka kawai Da dai bandi yaga abu yaci tura sai kawai yacewa hassu "tashi kuje bayin kiyi mishi ina zuwa. Chogewa hassu tayi ta tsaya tana kallonshi, tsawa bandi ya daka mata kin wuce kun tafi ko kuwa? Wato ina wasa dake ko? Ai duk ke kikace kinason a daukoshi a taimake shi don haka duk abinda ya kwaso kanki zai kare.... *Ina yiwa kowa fatan Alkhairi, kuma ina fatan kowa yana lafiya, kwana biyu kunjini shiru, anyi mana rasuwa ne* *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ🎀🎀* *Episode 37* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Da sauri hassu tayi hanyar shingen da suke hura wuta, tukunya ta samu ta ɗora ruwan bayan ta hura wutar. Shi dai sarfraz yana biye da ita duk motsin da tayi. Shi kuma bandi yana gefe sai dariya yakeyi yanaso yaga yanda abun Zai ƙare, koda ruwan yayi zafi sai ta ɗauki babbar robar da sukeyin wanka da ita ta juya ruwan zafin sannan takai bayi. Gurin bandi ta ƙarasa ta tsaya ɗan nesa dashi tace "banda na dafa ruwan" Gumtse dariyar dake bakinshi yayi "to ina ruwana, kije kiyi mata mana! Tunda dama abokinkice Juyawa tayi batare da tace komai ba, Sabulu da soso ta ɗauka a inda suke ajiye ta kama hannun sarfraz bata kuma ko kallon inda bandi yakeba, har cikin bayin inda suka ajiye dutsen da suke zama ta kai sarfraz tasa ya zauna a dutsen, sannan daga bisani ta cire mishi riga da dogon wandonshi sai tabar gajeren ajikin shi. Ganin ta nufi bayin batace komaiba yasa bandi miƙewa hade da fargabar Allah yasa ba wankan zatayi mishi ba, cikin sanɗa ya karasa gurin bayin ya leƙa . Har wata ajiyar zuciya ya sauke me nauyin gaske ganin irin dabarar da hassu tayi, shi dama wasa yakeyi mata yasone tayita bashi hakuri shi kuma yayi ta ja mata rai... Lafiyar Allah aka gama wankan suka koma ɗaki, akwatin ƙarfen da bandi yake zuba kayanshi ta buɗe ta zaɓi me kyau sannan ta bashi tace "zan fita kafin na dawo kicire wannan jikakken wandon kisa waɗan nan kayan. Waje ta fita ko kallon inda bandi yake batayiba Saboda Abinda yayi mata ya ɓata mata rai, shikuma ta gurin bandi ji yayi wata fargaba ta kamashi saboda fushin hassu baida kyau don sai su wuni su kwana bazata kulashi ba. A hankali ya karaso kusa da ita "hassu sannu da kokari ashe kinzata da gaske nakeyi? Nifa wasa nake Miki so nake inga yanda zakiyi! "Ai kaga yadda nayin Koh" haka tace batare data kalli inda yake a tsaye ba, sannan ta daɗa murtuke fuskarta... Fitowa SARFRAZ yayi jikinshi sanye da kayan bandi, abin gwanin ban dariya saboda Sam basuyi mishi ba duk a ɗingile duba da irin girman jikin SARFRAZ ɗin... Itama shiryawa tayi ta kama hannun sarfraz din suka nufi gidan Malam, ganin yadda hassu ta ɗauki zafi yasa bandi be kulataba illa shima sai yayi sauri ya shirya sannan yabi bayansu.... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Tunda tai sallar asbah bata tashi a saman dadduma ba, azkhar taitayi tare da addu'oi tana fatan Allah ya bayyana sarfraz sannan Allah ya kawo mata hanyar da zata koma gida taci gaba da yin rayuwarta kamar da. Wata irin ƙullewa cikinta yayi kasancewar yunwar da takeji, gashi jiya da dare babu yanda ba'a yi da itaba akan taci wani abuba amma taki. Kallon su mummy tayi taga sunata barci itada Aseey dayake muhsien a gurin Aayaan ya kwana. Ledar da Aayaan ya ajiye mata jiya da dare ta janyo sannan ta buɗe ta a hankali.... Kwalalo ido waje tayi ganin tulin chocolate da ice cream duk sun huce ma sun zama ruwa kasancewar ba'a sasu a fridge ba. Murmushi ne ya kufce mata batare data shirya zuwanshiba. Robar ice cream ɗaya ta dauka ta kafata a bakinta Saida ta shanye sannan ta cire robar.. Chocolate ɗin ta ɗiba da yawa ta zuba a cikin aljihun rigar ta sannan ta maida ledar ta ajiye.... Miƙewa tayi a hankali kasancewar kafarta Tayi tsami saboda daɗewa da tayi a zaune. A hankali ta buɗe ƙofar ta fita saboda bataso ta tashesu daga barci, shiru faloun babu kowa hakan yasa taji sha'awar ta fita harabar gidan taɗan miƙe kafarta. Hanyar garden ta nufa tana tafe a hankali kamar batason zuwa har ta isa dai dai wata bishiyar mango babba, a ƙasanta garden chairs ne jere guda biyar, a saman ɗaya daga cikin su ta zauna tana ɗan waige waige daga nan kuma ta faɗa duniyar tunani Aayann dake bakin window ɗin ɗakin sarfraz tsaye, yana kallon Nawaz tundaga fitowar ta har shigar ta garden ɗin. Samun kanshi yayi da son bin bayanta ko don yaga kyakkyawar fuskar ta da takeson hanashi saƙat. Be jira komaiba kawai ya fita daga ɗakin ya nufi garden ɗin, Nawaz dake zaune zuciyarta ta lula can cikin duniyar tunani sam tama manta a inda take sai jin Muryar Aayaan tayi yana cewa "Barka da safiya sister hope dai Lafiya kika fito nan da safen nan" Bayan kirjinta daya buga Saida jikinta ya dauki rawa kamar mazari, da kyar ta saita kanta sannan ta iya cewa "babu Komai! Ina kwana" A Kujerar dake gefenta ya zauna sannan yace "lafiya lau ya kika tashi? A hankali tace "lafiya lau" haɗe da mikewa tsaye Wai Nawaz meyasa sam bakyaso na raɓe ki? Kuma bakyaso mu zauna a inuwa ɗaya? Ganin shima ya miƙe yasa kawai Nawaz ta ruga da gudu zuwa cikin faloun. Dariya Aayaan ya ƙyalƙyale da ita "oh my God wai meke damun Nawaz ne haka? Jiyama daga shiga dakin ta shige bayi. Shafa fuskarshi yayi yana jinshi cike da nishaɗi sannan shima ya nufi hanyar komawa ɗakin... Koda Nawaz ta koma faloun bata tsaya ako inaba sai a kitchen... Tsayawa tayi tai shiru don jin motsin ko Aayaan ya biyota.... Takai minti biyar bata ji motsin kowa ba sai kawai tace bari ta koma daki, har ta kusa fita daga kitchen ɗin sai taga ai Gara da sama musu break fast tunda babu wanda ya tashi a gidan. Babban freezer ɗin dake cikin kitchen ɗin ta buɗe, tsayawa tayi ta zubawa cikin fridge ɗin ido tana nazarin abubuwan dake ciki. Kayan dazata buƙata ta ɗiba ta rufe fridge ɗin sannan ta shiga store ta kwaso sauran kayan da zata haɗa, ta yanke shawarar zatayi yam wages da potatoes omelet... Sai kunun gyada. Hankalinta yayi nisa sosai a aikinta don har tayi fin rabi sai kuma jin Muryar Aayaan tayi Yana cewa "sannu da aiki sister, duk kin cika gidan da kamshi me dadi. Murmushi tayi amma taɗan daburce, sai dai tayi ƙoƙarin ɓoye hakan. Kusa da ita ya matsa sosai "yauwa a faɗa min amsar tambayata ta rannan! Baya tayi ya kuma Binta, haka ta riƙa yin baya har Saida ta haɗu da drawer tukuna ta hakura shima rumfa yayi mata yana cewa "yanzu wa na kama? Ai duk taketaken ki ina sane dake! Ki faɗa min amsar rannan sannan kuma ki faɗa min meyasa kike min kallon dodo? Har gudu kikeyi idan kika ganni. Duk ta hargitse ga wani mugun tsoro dayake neman ya buga mata zuciya, har sautin bugun zuciyarta tana jiyowa kamar zata fasa kirjinta ta fito.... "Oh gosh!! Wai duka wannan tsoron na menene? Na taba yi Miki wani abune da Bakya so? "A'a" Nawaz tace tana goge zufar data tsatstsafo mata a gaban goshi Haɗa hannunshi yayi guri ɗaya 🙏 pls and please Nawaz kidena jin tsorona, idan muka cigaba a haka za'a fara zargina pls Gaba daya ya ƙureta domin harta da numfashinsu ya gauraye guri ɗaya, burinta be wuce ya matsa ta wuce ba... "To zan Dena Amma ka matsa in wuce" Ɗan matsawa yayi ɗin ta wuce sai kawai yaga ta kwasa a guje da nufin tayi falour, kasancewar shi soja kuma gwanin gudu hakan yasa taku biyu yayi ya chafketa, ai kuwa take ta faɗo saman kirjinshi. Mutsu mutsu ta fara tana cewa "ni dai ka sakeni Allah idan baka Dena kulaniba Zaku nemeni ku rasa, wallahi zan gudu, Shi kuma matseta yayi dakyau yana cewa "Ni kuma sai kin faɗi Dalilin da yasa kika maidani dodo! Ƙara yaji alamun za'a buɗe kofa, ai cikin hanzari yayi sama da ita kamar ya daga jinjiri ya koma kitchen ɗin cikin azama. Suna shiga ya sauketa amma be saki hannunta ba "nifa gaskiya ka dena yimin irin wannan, fisbilillah ka maida mutum kamar wata yar tsana, binibini ka daukeni! Gaskiya ka bari banaso, kuma wallhi idan ka matsamin ko Abujan bazaniba! Daya hannunta ya kamo ya riƙe ya haɗa duka biyun cikin nashi "pls and pls kada kice haka nidai sam banason tsorona da kikejine nafison ki saki jikinki Dani domin Ni yayankine. "Naji sakin mini hannu to" Nawaz tace tana murguɗa baki "Ni kike murguɗa wa baki? Idan kika kuma saina cinye bakin! "Nidai ka sakeni pls" Sakinta yayi yana murmushi don yasan daƙyar idan zata tsaya, ai kuwa da gudu ta ruga shima ya bita yana take mata baya... Dai dai zata buɗe kofa Aseey ta buɗe ai cikin rawar jiki ta faɗa jikin Aseey tana sauke ajiyar zuciya "Lafiya kuwa Nawaz? Meya sameki? Menene? Duka Aseey ta jera mata tambayoyin "Yaya Aayaann ne! Nawaz tace hawaye yana zubowa a idonta, "meya Miki? "Be min komaiba, ni kawai tsoronshi nakeji banaso yana zuwa gurina amma shi sai yayita zuwa. Aayann dake tsaye a bayanta yace "kuma bazan denaba har sai randa kika faɗa min meyasa kikejin tsoron nawa ba. Zubura Nawaz tayi zata shiga ɗakin don bata san Aayaann yana gurin ba, daƙyar Aseey ta riƙe ta "tsaya Nawaz kidena biye mishi so yake ya rainaki. Marairaice fuska tayi "Aunty Don Allah ki bari na shiga ciki sai muyi maganar anjima, matsa mata Aseey tayi tana mamakin wai meyasa Nawaz takejin tsoron Aayaan ne haka.. Shikuma yana tsaye yana murmushi, shidai kome zatayi burgeshi takeyi, musamman idan tana abun yarinta... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ta chan bangaren baffa (kakan Nawaz) yaje ya samu mahaifin baban Nawaz ya faɗa mishi cewa akwai wani jikanshi dayake neman Nawaz ɗin da aure kuma ya shirya, Hamdala sosai baba'Ango yayi domin ya daɗe yanaso ayi auren Nawaz ɗin tun kafin a nemi mahaifinta a rasa. Cewa baffan yayi "Aminina ai nabar maka Komai a hannun ka, kuma a matsayina na mahaifin Abban Nawaz na baka walicinta duk sanda yaron ya buƙata kawai a daura auren ko ta waya saika sanarmin tunda kace yaron na gida ne, Anan kuma saina sanar musu suje chan wajen ka ayi taron bikin ko? "Alhamdulillah Nagode sosai Aminina da wannan damar daka bani, kuma INSHA Allah Alkhairi zai zame mana sosai..... Dariya baba'Ango yayi "ai ko baka faɗa ba Nasan insha Allah bazanji kunya ba tunda yau sama da shekara hamsin munatare amma alkhairi ne ke zuwar mana ta dalilin juna. Bayan sun gama tattaunawa baffa yayi mishi sallama ya tafi zuciyarshi fal farin ciki, yana duba cewa ƙudirin daya dauka zai yiwu bada jimawaba. Waya ya dauka yasa Nura ya kira mishi Mummyn Aayaan domin su tattauna yadda abin zai wakana. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Kwana biyu bamu leƙa wajen umma ba👀👀 A Cikin daki na hangi umma tana Safa da marwa, da alamu tana jiran wani abu ne. Fauziyya ce ta fito daga bayi ta shiga ɗakin, "Yauwa fauziyya kin haƙa ramin kin binne? Umma tace jikinta na rawa. Eh na binne umma, "yauwa ai insha Allah Rahmatu bazata dawo gidan nan ba, kuma ita Nawaz ɗin databa wani dama har yana dukana to wallahi ta daki aurenta sai dai idan anayi a kabari tayi . Nifa sam na rasa meyasa na tsani Nawaz da mamarta? " Kinjiki da wata magana umma saboda ta aure Miki miji mana.. Fauziyya tace tana kashe ido daya Tafawa sukayi suna dariya kamar sa'annin juna.... *Kai umma Ni na rasa meyasa wasu suke ɗaukar kishi da zafi ne* _Kuma yauma idan kun karanta saura Kada kuyi comment👀, zakuji wayam ne gobe don hutun wata ɗaya zan ɗauka_🤗🤗 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ🎀🎀* *Episode 38* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Shiga dakin da Nawaz tayi yayi dai dai da gama wayar mummyn Aayaan ita da baffa, Yadda mummy taga Nawaz ɗin a hargitse yasa tace "matso nan daughter na! meya faru dake? "Murmushi Nawaz ɗin ta ƙaƙalo Wanda be wuce iya leɓe ba tace "mummy babu komai" Daidai Aseey ta dawo cikin ɗakin tace "mummy Allah da Komai Aayaan ne yake takura mata wallahi, yanzu fa daga kitchen nake naje na tarar abincin harya fara ƙonewa. Daram gaban mummy ya faɗi saboda ita tafison su fahimci juna, domin idan basu fahimci junaba taya zaman aure zai yiwu "me Aayaan ɗin yake mata? "Ban saniba gaskiya saidai wannan kusan shine karo na uku dana kamashi yana firgita ta" Nawaz tace " A'a mum bawai wani abu daban yakeyi mini ba, wani zubin idan ina aikine kawai sai inga inuwar mutum to Ni kuma sai in firgita.... Sosai mummy taji daɗin kare Aayaan da Nawaz tayi, hakan yana nuna zata zama macen kwarai mai ɓoye sirrin mijinta ga dukkan alamu.. "Nawaz na fahimceki kema sak Aayaan ɗin ce, kuyita fama da abu a zuciya bazaku faɗa ko kwa samu sauƙi ba. Ita kanta Aseey taji daɗi domin tana yiwa Aayaan fatan ya samu Nawaz a matsayin mata. Muhsien ne ya Turo ƙofar ya shigo yana tangaɗi alamun barci bai isheshiba, gefen da Nawaz ke zaune ya zauna yana mutstsike ido "Aunty kimin wanka please, Uncle ne yace wai zaki rakamu muga gari... "Zanyi maka wanka, amma yawo saikun dawo don banida lafiya. Shiru muhsien yayi tunda ta yarda zatayi wankan, koma meye ayi daga baya... "To isasshe! Wato kana kallon kowa amma babu Wanda ka iya cewa sannu sai faman bada doka da order, bazatayi wankan ba! Kyaɓe fuska yayi "to ina kwana mummy? Harara ta zabga mishi "Ni zaka fara gaisarwa? "Au mummy babba ina kwana? Murmushi mummyn Aayaan tayi "lafiya lau megida fatan ka tashi Lafiya! Murmushi yayi shima daga bisani ya gaida mummyn shi sannan ya gaida Nawaz .. Kama hannun muhsien Nawaz tayi ta shiga dashi bathroom ɗin Cikin Dakin.. Mummy kuma ta ciro wayarta ta ɗanyi danne danne sannan ta kara a kunne " wa'alaikumus salaam baba, okay to Babu komai dama nacene kawai a daura yau ɗin Allah ya tabbatar mana da Alkhairi.... Kashe wayar tayi cikin farin ciki, kana kallon fuskarta zaka gane kwanciyar hankali taysamu matsuguni a cikinta, domin sai murmushi takeyi .. "Mummy me za'a daura? Nifa ban gane wayar da kika gama yiba" Aseey tace tana kallon Mummy don jin ƙarin bayani.. "Ikon Allah!! Sai kuma akace komaine saikun gane Koh? Tunda mutum ya haifeku shikenan shi bashida sirrin kanshi Koh? "A'a Mummy kiyi hakuri ba haka nake nufiba wallahi, kawai dai maganar ce naji tamini wani iri. "To tashi ki bani guri tunda kin Zama Yar jarida, mummy tace tana miƙewa. Falour mummy ta fito tanaso suyi magana da Mummyn sarfraz amma har yanzu bata fito daga sashen daddyn sarfraz ba . Ta ɓangaren Aayaan kuma wanka yasha da wata irin bugaggiyar shadda saƙar Australia asalin waterproof getzner wadda ya haɗo a cikin kayan shi daga gida, gaba ɗaya kwarjinin shi da zallar kirarshi ta mazantaka saida ta bayyana duba da faffaɗan kirjinshi da cikakken damtsen shi, das kayan suka zauna mishi kamar a jikinshi aka tsara su, fuskarshi dake dauke da dara daran idanu da dogon hanci har zuwa bakinshi mai tudu wanda ya ɗan yi faɗi daga kasa, sai lips dinshi waɗanda suke pink amma sun sirka da ruwan ƙasa ƙasa, saje da ƙasumbarsa kuwa dama a gyare suke sai ƙyallin gyara sukeyi, shikaɗai yau yake jinshi cikin wani irin sihirtaccen farinciki Daka kalleshi kaga chocolate skin Pakistani.... Turarukanshi waɗanda suka zame mishi jiki suya kwaso ya fara fesawa tundaga kan body spray har zuwa cloth fragrance...... Shi kadai yake sakin murmushi don jinshi yakeyi sakayau, falour ya fito be tarar da kowa ba kai tsaye kawai sai ya wuce dakin dasu mummy suka sauka.... A hankali ya tura kofar ya shiga, babu kowa a ɗakin illa Nawaz wadda ta juya baya tana shafawa muhsien mai.. Bata damu data juyo ba domin a tunaninta Aseey ce ta dawo daga kitchen Kasancewar mummy tashiga yin wanka itama.... Tsaye yayi a bayanta yana kare mata kallo "Lallai Allah yayi baiwar halitta anan gurin, mamakin yanayinta yake yi yau sosai domin ko farkon ganinta da yayi be lura da Irin halittar jikintaba Kasancewar ana cikin tashin hakali. Amma yau tsaff ya ƙare mata kallo iya iyawarsa yana fatan Allah yasa ta Zamo mishi mahaɗin ruhi.. Nawaz dakeji kamar ido nabinta a jikinta sai ta ce "Aunty halan kin fasa cin abincin ne? "Nine ba Aunty bace" Aayaan yace with full confidence, da wani irin razani Nawaz ta waigo kirjinta na bugawa kamar zuciyarta zatayo waje Baya tayi tana tunanin yadda zata kaucewa kallon dayake yi mata, kunyar kanta ne ya kamata kasancewar rigar jikinta robace kuma tsaff tabi duk wani lungu da saƙo na jikinta ta lafe. Rurrufe kirjinta ta fara yi cikin dabara "nifa Malam kaga ka fita gaskiya, "idan naƙi fa? Aayann yace yana daɗa nufota haɗe da ƙara ƙare mata kallo..... Baya tayi tana nuna shi da yatsa "Malam ka fita nace inba haka ba Allah zanyi maka ihu. Daɗa matsota yakeyi yana cewa to saimene idan kinyi ihun? Aini dama nafison kowa yazo ya gammu a haka. Sosai ya hadeta da bangon wardrobe yana nufar cute pink lips ɗinta da nashi lips ɗin, ita kam Nawaz jitake inama ta mutu ta huta! Wai meye Aayaan yakeyi mata haka ne, shin wai besan yadda turarenshi ke hanata sukuni bane, kashe mata jiki yakeyi ya hanata sakat.... Ganin kuma kamar yanaso ya sunbace yasa tace "wayyo mummy" iya karfinta. Ai kuwa da gudu mummyn ta fito daga bayi dama dai dai ta gama wankan kenan, Ganin yadda Aayaann yayi mata rumfa yasa Mummy tace "ƙaniyarka Aayaan! Banason wulaƙanci fa, Wayace ma kashigo ɗakin? Me zakayi mata? Nifa banason fitina.. Ɗan daburcewa Aayaan yayi Kasancewar be zaci mummy tana dakinba sai kuma yace "mummy dama nazone nace ta shirya zata rakamu masallacin juma'a tunda Kinga bamusaniba, ita kuma yar garin ce. "Ohooo wato a yanda na ganka tare da ita shine kake tambayar ta, Aayaan ka kiyayeni ya mukayi dakai? "Sorry Mummy bazan sakeba INSHA ALLAH " "Wallahi kama sake" mummy tace tana balla mishi harara, sai Sannan ya buɗe ƙofar ya fita daga ɗakin.. Wata irin nannauyar ajiyar zuciya Nawaz ta sauke tare da fezar da iska mai dumi daga bakinta... Mummy ce ta nuna mata kusa da ita " xoki zauna anan daughter! Salalaf ta kama hannun muhsien ta tawo ta zauna kusa da mummyn, tare dajin nauyinta cikin zuciyarta. "Nawaz don Allah ki Dena jin tsoron Aayaan, daɗi fa yakeji idan yaga kinajin tsoronshi shiyasa yake daɗa shiga harkar ki, amma idan kika share kika nuna mishi Bakya wani jin tsoron shi duk zai dena takuramiki kinji my daughter? "To Mummy! Amma mummy nifa tun farkon dana fara ganinshi nakejin tsoronshi, "Af nace Miki dole ma ki marzaye, inba haka ba kisha wuya .... "To mummy" Nawaz tace tana nufar bayi itama don watsa ruwa Bayan ta shigane aseey ta shigo tana murmushi "Mummy Kinga Aayaan kuwa yau? Yadda kikasan wanda ake daurawa aure yau, wallahi kamar ango fuskarshi har wani ƙyallin kyau takeyi... Balla mata harara mummy tayi don tsaff ta gane nufin Aseey ɗin, so take dole saitaji menene wayar da Mummyn tayi dazu... "Come on wuce ki bani guri, maza ki shirya muhsien °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Shiryawa baffa yayi ya nufi gidan kakan Aayaan shida Nura da sauran fadawa don achan za'a ɗaura auren, domin duk sun gama maganar komai a waya har an sanar a masallaci cewa bayan sallar juma'a akwai daurin auren jikar hakimi. Sosai ake taron bikin amma Sam an kasa samun wanda zai faɗa wa Nawaz, domin sosai baffan yaja musu kunne akan kada wanda ya sake ya faɗa mata har sai sun fahimci juna. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Hakanan Nawaz takejin komai ya fita kanta ga wata iriyar faduwar gaba data addabeta, a sanyaye take komai domin koda ta fito bayin sanye da hijab kasa komai tayi ta nemi guri ta zauna tana sauraron bugun zuciyarta.... Da murmushi Mummyn SARFRAZ ta shigo dakin rike da wata shopping bag sai mummyn Aayaan itama tana biye da ita a baya,. Gefen Nawaz ta zauna "daughter ga kaya kisa kinji! Gwalalo Ido Nawaz tayi tana kallon wata iriyar shadda mai maiƙo sai kyalli takeyi tasha swarovski stoneworks da phoenix design "ni zansa Wannan? "Eh daughter takice wadda SARFRAZ ya dinka muku har kin manta? "Itadai Nawaz bata san wata shadda da sarfraz ya Dinka musu ba amma ko don DARAJAR sunan sarfraz ɗin da aka ambata aita saka. Amsar shaddar tayi tana murmushi, nan kuma Mummyn SARFRAZ ta Kalli mummyn Aayaan sukayi murmushin manya wanda su kadai suka san manufarshi. Fita sukayi daga ɗakin don ta samu damar shiryawa, abin yaba Nawaz mamaki domin kayan cif sukayi mata kuma sunyi das a jikinta, ita tadai sane don SARFRAZ amma bata jin wata walwala Tare Da ita .. Binta sukayi da kallo sanda ta fito falour domin wani irin haske ta ƙara ga wani kyau da tayi daga ALLAH. Aseey dai sai ido domin akwai abinda take hasashen amma mummy taki bata dama kuma ta taka mata burki. Mummyn SARFRAZ ce ta kwalawa Aayaan kira "To Aayaan ka fito ta shirya, kuzo ta rakaku masallacin lokaci yana ƙurewa.. Koda ya fito kasa boye mamakinshi yayi haka ya saki baki yabi Nawaz da kallon yanajin kamar yaje ya rungumeta ya maida ita ciki... GYARAN murya Mummy tayi sannan tace "ku tafi mana ko sai kun makara? Gaba ɗaya Nawaz ta shiga damuwa wai fisbilillah yaza ayi aita hadata a Aayaan bayan Ansan basa jituwa. Ɗaki ta koma ta dauko babban mayafin da Mummy ta haɗo mata Tare Da shaddar ta fito ta bisu parking space. Tundaga nesa ta hango Aayaan ɗin yadda yayi wani irin mugun kyau, cikar kamala da kwarjini, haka nan ta kasa jure kallonshi duk da kasancewar suna nesa, koda ta karasa motar ta shiga bata tanka suba sannan duk suka shiga suka dau hanya ... Masallacin Albani takaisu inda ita ta zauna a cikin motar tana jiransu, yayin da kuma ƙarfe ɗaya da rabi daidai ta tsinci wata irin karayar zuciya ga kirjinta da yayi mata nauyi kamar an ɗora mata wani Nauyi nadaban ... Sannan bugun zuciyarta ya ƙara tsananta. Shi kuwa ta ɓangaren Aayaann yayi dai-dai da sun fito daga masallaci abokinshi Junaid Ya kirashi a waya, sai murmushi hakeyi kamar gonar auduga... Cikin annashuwa ya shiga motar yana faman zuba wani irin killer smile, Mamaki abin yaba Nawaz lallai duniya juyin juyi ce, ita ga halin da take ciki shikuma dariya ma yakeyi alamun Duniyar tai mishi daɗi. Lura da Irin kallon da take mishi yayi, kashe mata ido yayi haɗe da daga mata gira "Toya maman boy ko akwai abinda kike buƙata ne Kinga yaro dan dagwas dani. Taɓe baki Nawaz tayi "kai ɗin ne dagwas? Lallai kana kallon ka kamar wani basmude zaka ce wai kai ɗin dagwas ne, ina tausaya matar ka Wallahi Donna lura ka cika salo da salsala..... Wace matar tawa kike n........ *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 39* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji*✍️ Wace matar tawa kike nufi? Balla mishi harara Nawaz tayi "au matan naka har nawane da zakace saina banbance maka wacce daga ciki.. " Hmmm yarinya zaki sani ne, wato kin fara rainani Koh? Murguɗa Baki Nawaz tayi "niba yarinya bace" "Au ashefa sunanki maman boy ko? Sorry na manta" "Eh sunana haka ɗin saime?" Wajen muhsien ta waiga "muhsien ɗana zoka zauna a cinyarta kaji daga yau sunana mummynka" Cinyarta muhsien ya dawo yana kallon fuskarta "Aunty da gaske kema mamana ce? Murmushi tayi mishi "eh muhsien, Nima mamankace kaji?" Aayann kam sakin baki yayi yana kallonta "wai ɗan ta bata min rai take wannan? Murmushi yayi kawai be kulataba ya tada motar yayi gaba.. Dai dai sunzo zasu wuce layin baaba Ahmad Nawaz tace "Please anan gaba kaɗan akwai gidan wata ƙawata Nafisa tare mukayi Junior secondary school da ita idan ba damuwa dan Allah inaso kaɗan tsaya zan shiga mu gaisa. "Okay babu matsala nunamin inda zamubi. Dai dai Kofar gate ɗin gidan yayi Parking Sannan Nawaz ta fito riƙe da hannun muhsien, shima sai ya fito ta ɗaya ƙofar ya jingina da motar yana kallon Nawaz ɗin, wacce tayi wani irin shu'umin kyau, "ku shiga Ni zan tsaya daga nan in ɗan ga gari. "To" Nawaz tace tare da tura gate ɗin suna shiga ciki. Durkushe Nafisa take tana Alwala taji an buɗe gate an shigo, da sauri da ɗago kai don ganin waye, Aikuwa da gudu ta saki butar ta nufi Nawaz ta ruƙunƙumeta "wayyooo Allah yau juma'ar ta musamman ce, Nawaz kece? Wallahi nayi kewarki. Babu abinda Nawaz take yi sai murmushi, Sakinta Nafisa tayi Sannan ta Kama hannun muhsin suka shiga ɗaki, a kujera ta zaunar dashi sannan ta kwaso kayan ciye ciye kala kala na yara ta miƙa mishi, ita kuma Nawaz ta kawo mata drinks. "Oh Nawaz ashe rai kanga rai? Aini Nasha munyi hannun riga bazamu sake haɗuwa ba, kinsan rabonda mu haɗu tun bikina, Gashi dama Ni bansan gidankuba kuma numberki bata shiga. Hmm wallahi kuwa, Nima abubuwane sukamun yawa kinsan fa bayan Nagama NCE Saida na ɗora da B.ED. "Ikon Allah kice kunbarmu a baya, nida nayi aure a jss3 kinsan bebari naci gaba ba. "Haka ne Allah kinsan wasu mazan basason suga matansu suna zirga zirga cikin maza. Cewar Nawaz tana daukar ruwa "Wallahi kam, Allah dai ya bamu zaman Lafiya a gidajen aurenmu ya kaɗe fitina. Nawaz tace "Ameen tana ajiye Ruwan bayan ta kurɓa, "wai kuwa yaranki nawa yanzu? Dariya Nafisa tayi "yarana biyar" 😳 Eyee wai wasa kike ko gaske? Amma Nafisa kece da ya'ya biyar? Nawaz tace cike da mamaki. "Wallahi dagaske nake, saidai haihuwata huɗu, saboda Akwai ƴan biyu shiyasa ƴaƴan suka zama biyar. Murmushi Nawaz tayi "haba koda naji amma ko a huɗun ma sunyi yawa, inasuke?. "Kai Nawaz ko don ke haihuwar ƴan gayu kikeyi? Suna gidan kakansu. "Hmmm aini banyi aureba har yanzu, sai dai ku taysamu da addu'a. Da suna nan Aida na gansu "Harara ta balla mata, lallai NAWAZ aiko makaho ya shafa fuskar ɗan nan ya shafa taki yasan kece mamar shi balle Nida Nasan yawan shekarunki, tundama shekara biyu na baki Kinga kuwa yanzu ina 27 Kinga ke kina 25 kenan. "Dariya Nawaz tayi kinsan Aure lokacine, har yanzu dai munanan Muna jiran rabbil izzati, amma Allah banyi aureba har yanzu ki yarda dani. "Wai Nawaz meye abin jin kunyata? Inkinyi aurenmu meye? Kallon muhsien tayi "yarona ya sunanka? Haɗiye biscuits din daya cika bakinshi dashi yayi Sannan yace "sunana muhsin" Murmushi Nafisa tayi "Nice name! Kuma da alamu kaima irin kwakwalwar mamanka kayi. Dariya Nawaz tayi "wai kinƙi yarda da magana ta Koh? "Yaza'ayi in yarda, Muhsin waye mamanka? Nuna Nawaz yayi Sannan yace "wannan ce" Zaro ido waje tayi "muhsin banason ƙarya, Ni mamanka ce? Murmushi muhsien ya daɗa yi yace "wallahi kece" Kyalkyale wa da dariya Nafisa tayi "to kindaiji yaro baisan karya ba, kada ki koya mishi. Mamaki gaba ɗaya ya cika Nawaz shiko meyasa muhsien yace haka, "Nafisa inaga zamuzo mutafi yaya Aayaann yana jiranmu a waje! "Subhanallah Nawaz bakida mutunci, ashe tare kuke shine ko ruwa baki kaimai ba? " Mtsewwwss inaga koda nakai bazai wani shaba, yauwa muje wajen saiki tambayeshi waye mamar muhsien ɗin, kila idan shi ya faɗin miki ki yarda. Kama hannun muhsin tayi suka fito tsakar gida Sannan ta ɗauki hijabinta dake saƙale a igiya tasa, Nawaz kuma tana binsu a baya. Mamaki abin yaba Nafisa sosai, yadda taga Aayaan ɗin itama Saida ya burgeta matuka "inayini surukina" Murmushi Aayaan yayi "lafiya lau Babbar ƙawa, yau dai zan huta kuma za'a barni nayi bacci lafiya. "Murmushi Nafisa tayi tana daɗa mamakin a ina Nawaz ta samu mijin nunawa Sa'a irin Aayaan Sannan tace "sabodame kace haka? "Ai baki saniba tunda muka haɗu da ita ta faɗa min tanada wata kawa Nafisa tare wai kukayi jss da ita amma waike kinyi aure, wai kun shaku sosai. Baki da hanci Nawaz ta saki tana kallon Aayaan wanda ya zage yana haɗa karya. Ita kuma Nafisa sai tayi dariya jin dadin maganar da Aayaan yayi, wato tanada matsayi kenan. "To ai baki saniba, Lokacin biki ma haka ta matsamin, to amma dayake ba'a nan akayi bikin namuba shine na samu sauƙi, kuma in faɗa Miki ko data haifi muhsien bata barni na hutaba musamman ranar suna, to Kinga dole nace yau za'a barni na huta. Wata dariyar Nafisa ke daɗa yi "ikon Allah, Wallahi Nima inanan kusan kullum saita faɗo min araina wallahi, ashe nima ina maƙale a zuciyarta. Rungume Nawaz ɗin tayi "inasonka ƙawalliya" sannan tayi ƙasa da muryarta tace "Allah ya tona Miki asiri gashi tun ban tambayeshiba ya faɗamin da kanshi. Sannan ta saki Nawaz ɗin tana kashe mata ido. Itadai Nawaz tsaye take kawai tana kallon ikon Allah " wai dama haka Aayaan ɗin yake, Cikin ƙanƙanin Lokaci ya haɗa labari kamar a cinema. Shima Aayaan yana ankare da Nawaz hakan yasa ya daɗa cewa "amma kada ki damu wannan karan idan ta haihu har gida zansa azo a ɗaukeki kizo mana suna. " 😳 Allah sarki Nawaz ashe da wani rabon ma, Allah ya raba lafiya, gaskiya naji daɗi sosai wallahi, Allah dai ya ƙara zaunar damu lafiya. Ai Nawaz fashewa da kuka tayi kawai ta nufi mota bata kula suba, inbanda Tiƙuƙi babu abinda zuciyarta keyi, wato ita Aayaan zai haɗa wa sharri.. Shi kuma Aayaan ganin nawaz ta tafi yasa yacewa Nafisa "bari mu tafi, kinsan Madam ɗin tawa Sarkin shagwaɓace, kuma dama tunda ta samu Wannan cikin tace wai ita kunya takeji. "Hum aidama tun muna makaranta Nawaz Sarkin shagwaɓace, komai akayi sai tace umminta. Hannu Aayaan yasa a cikin aljihu ya ciro sababbin Yan dubu dubu wanda baisan adadinsuba ya mikawa Nafisa gashi a siya wa yara biscuits dukda ban gansuba. Da kyar Nafisa ta masa sannan tace eh ai basa nan duka suna gidan kakansu. "Masha Allah, Allah yayi musu albarka, a gaida megidan, saimun kuma waiwayoku nida Madam, Aayaan yace yana kama hannun muhsien zuwa cikin mota. Itama Nafisa ta koma gida tana mamakin Wannan mutum me sakin fuska haka, lallai Nawaz ta dace. Wiwiw ya tarar da Nawaz tana kuka gaba ɗaya idonta yayi ja, hakama fuskar tayi ja kamar kosai kasancewarta fara sosai "Haba maman muhsin meyasaki kuka? Wata uwar harara da Nawaz ta balla mishi Saida yayi murmushi Sannan tace "malam babu ruwanka dani kuma wallahi kaci gaba da tsokanata, Sannan na rantse da Allah bazanje abujarba kasan yanda zakayi dasu. Kuma ko kaƙi koh kaso gidanmu zan koma. "🤔 Ooh Nawaz ɗin tawa dama tana fushi? Ikon Allah aini Nasha Bakya fushi. Janyo ta yayi zuwa kirjinshi ya rungumeta tsam yadda bazata iya kwacewaba, mutsu mutsu ta rikayi tanaso ya saketa amma yaƙi Sakinta gashi ta kasa kwace kanta. Sai Kawai tayi shiru ta hakura donta lura wahalar da kanta zata yi. Kamshin turarenshi ne ya cika mata hanci gashi tanajin sound din bugun zuciyarshi da sauri da sauri, sai ɗumin jikinshi da a hankali ya fara ratsa nata jikin. Shima ta bangaren Aayann hakane, yana sauraren nata bugun zuciyar, ta ɓangaren shi kuma wata irin natsuwa yaji tana saukar mishi a hankali... Motsawa Nawaz ta kumayi "kaga gaskiya ya Aayaann ka sakeni kasan cewa hakan dakamin haram ne, kuma Nima nasan hakan. Cikin raunatarciyar murya yace "amma ai yin hakan ba haram bane a gurin ma'aurata ba ai. "Kaga kabar wannan wasan yaran da kakeyi, nidai ka rabu Dani, yaushe ka zama mijina? Nida banfi sati biyu da saninkaba... "Kasa Sakinta yayi don kasancewar su a hakan ya mishi daɗi sosai a zuciyar shi. *Auncle menene ya samu aunty Nawaz taketa kuka*? Muhsien yacewa Aayaan ganin anyi Banza dashi... "Batada lafiya ne shiyasa" Matsowa kusa da ita MUHSIEN yaayi yana taba bayanta a hankali "sannu mummyna kiyi hakuri Uncle zai kaiki asibiti kinji. "Yaya Aayaann pls ka sakeni na hakura" Nawaz tace jin abin yayi mata yawa Murmushi yayi "ashe kin gane abinda nake nufi, Sakinta yayi tayi baya tana gyara mayafinta amma duk jikinta yayi sanyi .. Kunna motar Aayaan yayi yana murmushi sannan yace "Madam yanzu gidan wace ƙawar taki zan rakaki. Kasancewar tana jin dan nauyinshi yasa tace "ai Ni inaga har abada nida in kuma cewa ka rakani wani guri. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° A chan gida Mummyn SARFRAZ ce zaune tare da Mummyn AAYAAN suna hirar aurensu Nawaz da aka Daura.. Mummyn sarfraz tace nifa tunda naga Aayaan wallahi naji kewar sarfraz ta ragunmini da kaso 40% Sunyi kama sosai kuma yanayin Mu'amular su iri ɗaya... Nidai fatana Allah ya nuna mana sarfraz a raye saboda inaso inga gudan jinin Yar uwata. Cewar mummyn Aayaan shiru Mummyn sarfraz tayi ta kasa cewa komai saboda jimami. "Amma gaskiya ki hana Aayaan zuwa da Nawaz Abuja ko Babu komai Kinga yanzu ita matar aurece bazai yiwu a baza hotonta a kowace kafar sada zumuntaba gaskiya" Mummy sarfraz tace. Wani irin tsallen murna Aseey wadda ke laɓe a bayan labule tayi, wato hasashen ta ya zama gaskiya kenan, Auren Aayaan da Nawaz aka Daura ɗazu kenan farinciki fall zuciyarta. Aayann ne rungume da muhsien sai Nawaz a gefe suka shigo cikin falourn, Assalamu alaikum barkanku da rana. "Sannunku da dawowa, kunga yadda mukayi matching kuwa Kamar mata da miji cewar Aseey tana ƙunshe dariya. Ita dai Nawaz batada Burin daya wuce taganta a ɗaki ta cire kayan jikinta saboda gaba ɗaya kamshin Aayaan takeyi Kuma gani takeyi za'a gane ya rungumeta.... *Bayan awanni shida...* Nawaz na zaune a falour kasancewar yau Aseey ta hanata sakat daga wannan sai wancan, mummy kuma suna chan sasan daddy kasancewar yau yayi tafiya. Tashi Aseey tayi"sweet sis bari nazo kinji? To Nawaz tace tana kallonta har ta shiga ɗaki. Aayaann dake labe a gefene ya fito ya nufi Nawaz a hankali, Saida yazo gabanta sannan ta ganshi... Tsugunawa yayi gabanta "dear inaso muyi magana dake me muhimmanci Please zo muje? "Waye zai bika? Malam kaga gaskiya ka fita harkar fa, ehe. Be jira komaiba ya suntumeta yayi hanyar ɗakin SARFRAZ rungume da ita sai wuntsil wuntsil takeyi Please ayi comments *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 40* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Saman gado ya ɗora ta yana murmushi "wai ke meyasa komai saikinyimin jayayyahne? samun sauƙi na daya shine zan iya ɗaukar ki, amma dabadon hakaba dana wahala ainun. Shiru Nawaz tayi tare da ƙarewa ɗakin kallo tana tuna ranar data fara shiga cikin shi, komai yayanan yadda yake illama ɗan gyare-gyare da aka samu, sai kuma ƙamshin Aayaan daya gauraye ɗakin saɓanin da kamshin SARFRAZ ne. Hakan ya daɗa tabbatar mata cewa Aayaan ba baya bane a wajen tsafta. "Hmmm kazo gidan mutane ka wani hakimce Koh? Sai kace ɗakin ka, to mai ɗakin dai yananan dawowa. Nawaz ta faɗa tana daɗa gyara zama a saman gadon Gabanta ya karaso ya ɗora hannuwanshi a saman cinyarta sannan ya tallabe haɓarshi dasu "ɗaki nane mana! Tunda ai ɗakin ƙaninane Koh? And kuma ni sainafi kowa jin daɗi muddin SARFRAZ ya bayyana. Ture hannuwanshi tayi daga kan cinyarta " Sannu malam! Allah duk jin daɗinka bazaka kaini ba, domin yanzu kaf cikin rayuwata babu abin dana sa agabana kamar fata da addu'a akan Allah ya nunamin SARFRAZ... Saida zuciyar Aayaan ta buga jin maganganun Nawaz, take ya fara zancen zuci "kada fa Nawaz son SARFRAZ takeyi? Idan kuwa hakane Nasan na makara ba lallai tasoni ba gaskiya. Amma a fili sai yace "Ni kike turewa daga jikinki Koh? Chuno bakinta tayi "nifa yaya Aayaann Wallahi banaso kana taɓa min jiki, amma naga kai hakan ya zame maka jiki Koh. Wani irin ƙayataccen smirking yayi Sannan cikin tausasasshiyar murya me kama da raɗa yace "yap i am addicted to your body, kuma kece kika sabarmin da hakan. "Kamarya? Nifa banason ƙage. Cewar Nawaz tana haɗe fuskarta "Wallahi ke kika koyamin, ki tuna fa duk sanda muka hau mota saikinyi barci a jikina kuma aƙalla ba'a ƙasaraba sai kinyi barcin sama da awa biyu. To ta ina kike tunanin jikina bazai saba da ɗumin jikinkiba? Miƙewa Nawaz tayi "Gaskiya ka shahara, nidai bani guri in wuce" Shima Aayaan sai ya Miƙe Kamar zai matsa ya bata guri sai kuma charaf ya rungumeta yana hadata da jikin bangon ɗakin. Kasancewar shi mai faɗin jiki da murdewa yasa duka ya rufeta, sannan a tsawo bata wuce iya kirjinshiba.. Tsoronshi data ɗan samu sauƙin shi ne ya dawo mata sabo fili, fat fat fat haka kirjinta ke bugawa, gaba ɗaya jikinta saiya kama rawa, cikin dasasshiya kuma shaƙaƙƙiyar murya tace "Don Allah yaya Aayaann kabari, Wallahi banaso. Shima ta bangaren Aayann bugun zuciyarshi ne ya karu kuma a hankali yakejin numfashin Nawaz yana sauka saman kirjinshi ga sautin bugun zuciyarta daya ƙaru alamun tsoro ƙarara ya kamata. "Nikuma inaso!" Abinda Aayaan ya iya cewa kenan cikin low tune. Cikin abinda bai wuce second hamsinba numfashinsu ya gauraye da kamshin turaren Aayaan da wanda itama Nawaz tasa, saiya bada wani irin romantic scent. Hakan yasa daƙyar Nawaz take iya jan nunfashi tanajin wata iriyar kasala na saukar mata a hankali, shikuwa goga Aayaan ji yake kamar a dauwama a haka saboda wani irin feelings Dake ratsashi Lokaci guda wanda be taɓa Experiencing ɗin irinshiba, hakan yasa jikin shi ya mutu tare da wata kasala shima data saukar mai. Kusan a Tare suka sauke wata iriyar raunanniyar ajihar zuciya. Tanaso tayi magana amma Sam bakinta ƴaki buɗuwa ya bata dama, sai kawai tayi yunkuri ta tattaro ragowar karfinta ta turashi baya. Cikin ikon Allah sai kawai taga yayin bayan kasancewar jikinshi daya saki gaba ɗaya. Aikuwa da sauri Cikin rashin kwarin jiki Nawaz tayi hanayar waje, sai Sannan shima yayi sauri don ya cin mata amma ina ta rigada ta buɗe ƙofar ta fita falour. "Madam please ki dawo, bamuyi maganar da nakeso muyi ba! wallahi i seriously need your support and Du'a. Kota kanshi Nawaz bata biba tayi hanyar dakinsu tanajin wata irin fargaba a zuciyarta. "Gaskiya zata dena ba Aayaan fuska, kada azo tsautsayi yasa wani abuu ya ratsa tsakaninsu ta shiga uku... Tana jiyoshi yana cewa "i promise bazan kuma hugging ɗinki ba, amma Please ki tsaya ki saurareni. Koda ta shiga dakin bataga Aseey ba, sai kawai ta nemi guri ta zauna kirjinta na cigaba da bugun tara-tara, hakanan takeji kamar har yanzu tana cikin jikin Aayaann ne, gashi duka jikinta ma kamshinsa yakeyi. Shi kuma Aayaan takaicine ya kamashi "meyasa na kasa control ɗin kaina ne, ohhh da kaina kuma nake shirin ɓatawa kaina Budget, amma naso muyi magana ko don naji ra'ayin ta. But never the less zanyi abinda ya dace kawai. Juyawa yayi da niyyar ya koma ɗaki sai yaga Aseey zaune tana murmushi. Ɗan daburcewa yayi "ehmm sis Ashe kina zaune? "Ina zaune tun ɗazu amma tsabar yanzu kazama mara kunya baka lura ma daniba, hmmm ai Wallahi na godewa Allah, domin ko yanzu ALLAH yabar ka Nasan ya ramawa tulin ƴan matan daka riƙa wulakantawa a makaranta... Bakada abinyi sai tozarta Mata musamman waɗanda kaga sunaso suriƙa shiga sabgarki. " To yanzu gashinan matar kace amma tsoronka takeji. Kusa da ita ya matso "sis wai don Allah dagaske mummy takeyi an daura mana aure yau? Nifa jin abun nakeyi Kamar a mafarki "Au dama mummy ta taɓa yi maka ƙaryane ban saniba? "No sis ba haka nake nufiba, kawai dai abin ne is very very amazing, ace wanna beautiful damsel ɗin tawace!. "hmmm kadaiji dashi, sannan INASON baka shawara ka mu'amulanceta cikin kwarewa da wayewa har Allah yasa ka dasa sonka kai ma a zuciyarta, amma idan ka rusa komai to nidai babu ruwana don naga alamar ka cika gaggawa. Focus on showing her real love And affection. Murmushi Aayaan yayi "THANKS sis, insha Allah i will try my very best, zan kiyaye bi'iznillah, i will be getting in kinsan abinda zanyi gobe Koh? "To ameen Allah ya bada iko, eh nasani Sweet dreams... Goodnight.. Ɗaki ya koma shima ya kwanta amma Sam ya kasa barci, yana mamakin yaushe sonta ya kamashi hakane, bayaso daidai da minti ɗaya yaga bata kusa dashi, ga kuma fargabar mezai biyo baya tunda yaga ranta ya ɓaci sosai.... Hakanan dai ya janyo pillow ya rungume yana sauke ajiyar zuciya... Koda Aseey taga Aayaan ya shiga ɗaki sai kawai itama ta miƙe tabi bayan Nawaz... A chukurkuɗe ta tarar da Nawaz ɗin ta cure jikinta guri ɗaya. "Sis meyafaru? Ɗazu danace Miki Ina zuwa sai na dawo kuma naga Bakya nan, Nawaz baza ta iya faɗin ma Aseey abinda ya faru ba saboda batason Aseey ta zargi wani abun a nata tunanin, sai kawai tacewa Aseey "waje na fita" Murmushi Aseey tayi tana jinjina zurfin ciki da kawaicin Nawaz, kusa da Nawaz ɗin ta karasa zata zauna, aikuwa da sauri Nawaz ta mike saboda batason taji kamshin Aayaan dake tashi a jikin ta. Tsaff Aseey ta gane me Nawaz ɗin take nufi amma saita basar kamar bata ganeba. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Kafin wannan lokacin 7hours back. Koda hassu suka isa gidan baffa malam basu sameshiba, shine suka shiga Asalin cikin gidan wajen adda bilki don suji ina yaje.. Bayan sun gaisa ne adda bilki tace "ba nisa yayi ba, kafin ya fita ma yace min idan kunzo ku jirashi. To hassu tace tare da zama a saman turmin dake gefe, shima SARFRAZ gefenta ya samu ya zauna yana rarraba Idanuwa. Suna zaune hassu taga Adda tana fita da wanke wanke da alamu yi zatai, da sauri ta mike tana cewa adda ki bari inyi Miki. Murmushi addan tayi tace "to hassu ga omon" batayi yunƙurin hana taba don tasan kome zatayi bazata iya hanata yin wanke wanken ba ɓata bakinta Kawai zatayi. Bayan hassu ta gama wanke wanken ne tana share tsakar gida baffa yayi sallama suka shigo shida bandi.... Dena sharar hassu tayi saboda kada ta watsa mushi ƙura haɗe da Basu guri su wuce, Sannan ta gaida shi cikin girmamawa... "Hassu na burge baffa malam domin ayanda ya lura yarinyar tanada hankali da ace yanada ɗa babba saiya aura mishi ita. Cikin fara'a ya amsa mata yana ƙara tambayarta yata kwana da mai jiki. Bayan Adda ta shimfiɗa mishi tabarma ya zauna ne yasa ta zubo musu ɗumamen Tuwon biski Wanda aka Wadata miyar da ganyayyaki da nama. "Ki zubowa hassu itama, idan tare zakuci kuma to! So nake idan muka gamaci mu wuce asibitin,Bandi ku wanko hannu kaida SARFRAZ kuzo muci tare. "Nida hassu zanci" SARFRAZ yace yana hararar baffan Murmushi baffan yayi haɗe da cewa "haba malam SARFRAZ ai abin bana faɗa bane, za'a zuba muku, bilki sa musu nasu tare kawai... "To" bilki tace tana komawa hanyar kitchen donyin yadda baffan ya umarce ta. Koda suka gamacin abincin nan suka wanke hannu sannan suka yiwa adda sallama suka fita, a waje suka tarar da mai adaidaitar da baffa malam yazo dashi yana zaune yana jiransu, Cikin motar ya koma ya zauna sannan malam ya zauna a gefen driver ɗin sukuma su bandi suka shiga baya, duk wannan abinda akeyi hassu ko kallon inda bandi yake batayi, ya matuƙar ɓata mata rai. A hankali suke tafiya har suka fita cikin gari inda suka isa general hospital ɗin dake cikin garin azare... Naanma baffan cewa drivern yayi ya jirasu sannan su suka shiga zuwa Cikin asibitin. Sashen psychiatric suka wuce don Ganin Babban likitan ƙwaƙwalwa, wanda shine zai duba SARFRAZ ɗin. Cewa akayi bazasu shiga dukansuba sai dai mara lafiyar shida mutum ɗaya, Kasancewar hassu tasan malam zai iya cewa bazai shiga ba yasa tayi saurin cewa baffa ka shiga idan ka fito sai ka faɗa mana yadda kukayi.. To baffa yace Sannan ya kama hannun sarfraz don shiga office ɗin. Amma Allan baran SARFRAZ yace shifa baisan zance ba, idan ba tare da hassu ba babu inda zashi... Hakanan likitan yace to a kira hassu ɗin saisu shiga tare saboda anason Babba a gurin yadda zaifi gane bayanan da likitan zaiyi.... Bayan ya ɗibi jinin SARFRAZ sai aka kwantar da shi saman wani gado, sannan aka haɗa allurori har guda biyar aka zuba a cikin normal saline aka sa mishi a hannu.. Likitan lab ne ya shigo riƙe da takarda yana goge zufa "Doctor akwai babbar matsala Wallahi. Pls comment and share *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 41* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Babban Doctorn ne yace "wace irin matsala kuma?" Kusa dashi ya ƙarasa yayi ƙasa da murya sukayi magana yadda su baffa bazasujiba. Shiru yayi yana tunanin yadda zai faɗawa su baffan wannan gagarumar magana, duba da yadda ya gansu yasan ba masu wadata bane. Natsuwa yayi sosai Sannan ya maida hankalinshi guri ɗaya yadda zai samu abinda zai musu bayani, sannan yayi gyaran murya " Baba ansamu Babbar matsala amma dai za'a iya maganceta. Baffa yace "likita faɗa min wace irin Matsala aka samu? Tun ɗazu kunata ƙus ƙus amma bakace mana komai ba! "Baba majinyacinmu ba ciwon mantau bane ya kamashi, kwakwalwar shice ta goce daga ma'ajiyar ta. Amma idan akayi aiki ana warkewa sai dai ba'a nan ƙasar akeyin aikinba. Wata zufa baffa yaji ta sauko mishi, "innalillahi wa'inna ilaihiraji'un! Lahaula wala quwwata illah billahil Aliyul azeem! Subhanallah! To likita yanzu ya za'a yi? Gyara zama likitan yayi yace "ai ba ita kaɗai bace matsalar! Bayan wannan akwai hormones imbalance a tare dashi, kuma bincike ya nuna ciwonma ya daɗe Abokinshi. A Tare hassu da baffa suka miƙe " likita badai kana nufin mutuwa zaiyi ba ko? Ɗan murmushi doctor yayi "kada ku damu bazai mutuba, yanzu dai ku koma ku zauna, abu ɗaya ne damuwar shine kudin da za'a fitar dashi ƙasar waje ayi aikin. "To likita kana ganin zai kai nawa? Baffa yace Yana daɗa daidaita nutsuwarshi. "Eh to gaskiya baba bazan ɓoye maka komaiba, waccan shekarar mun taɓa samun mai irin wannan matsalar, kuma gaskiya a yanda akayi lissafi sun kashe kuɗi yakai kimanin million goma sha uku. Miƙewa baffa yayi haɗe da cewa "iye! Na'am! Miliyan nawa? Tabɗi aini a halin yanzu ko dubu ɗari ta kaina banida ita balle million. "Calm down baba! Kada ka tada hankalinka, kasan komai Allah ya tsara ma bawa baya iya kauce mishi, yanzu abinda nakeso dakai shine ayita addu'a, saikaga Allah ya kawo wanda zai biya kudin aikin cikin sauƙi. "To Allah yasa! ta malam bata wuce Ameen, amma a ƙarnin nan waye zai iya biyan million goma sha biyu don ayiwa wani aiki? "Numfasawa Doctorn yayi "baba nace ka kwantar da hankalinka kuma kuyita addu'a, kuma inaso inyi maka albishir cewa akwai Wani babban soja da yake biyawa mutane kuɗi idan basuda hali, to shine nakeso idan yazo zanyi mishi bayani kila Allah yasa ya biya mishi. To shikenan likita mungode, amma yanzu babu wani abu da za'a bashi wanda zai iya taimaka mishi gurin lafiyar shi? Kaga kuma yanada ciwo a jikinshi. "A'a duka wannan babu matsala zan haɗa ku d wanda zai wanke mishi ciwon kuma zai baku magani. Miƙewa baffan yayi "to likita mungode! Tare suka fita duka zuciyarsu babu daɗi barin hassu da take ganin kamar bazai taba warkewa ba. Kamar yadda likitan yace haka aka yiwa SARFRAZ dressing ɗin ciwon aka basu magani suka tafi gida. Sai bayan sun koma gida ne baffa yayi wa bandi bayanin yadda sukayi da likita, shima bandi baiji daɗi ba, Sannan ya ƙara tausayawa sarfraz halin dayake ciki .. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Kallon Nawaz ɗin tayi tace "sis don Allah kada ki tafi ki barni! Take hankalin Nawaz ya koma kan Aseey "sis meyasa kikace haka? Ko wani yace Miki zan tafi gobe ne. "A'a Kawai dai ina rokon Alfarma ne akan ki zauna tare damu har zuwa sanda zan koma England, saboda duk sanda naganki ji nake kamar ke ɗin jini nace domin nida mummy munyi burin samun yar uwa mace amma dayake Allah ya riga da ya gama tsara komai sai bata kuma haifar maceba sai Aayaan da marigayi.. Kusa da ita Nawaz ta ƙarasa ta rungume ta, tama manta cewa batason taji kamshin turaren Aayaan daya gauraye jikinta kamar ita ta shafa "sister i feel your pain, Nima inada wannan tabon a zuciyata inaga har gara ke kinada ƙani nifa banida kowa. "Yea kin faɗi gaskiya, amma Nawaz me zai hana mu zamewa juna sisters! Kinga shikenan Ni sai na zame Miki yayar da kika daɗe kina nema, ke kuma saiki zamemin ƙanwar da na daɗe ina nema. Murmushi Nawaz tayi "yea big sis Nagode da wannan dama da kika bani, i really appreciate.. Sakin juna sukayi Sannan Aseey ta fara magana. "Sis Nawaz kinsan cewa mummy bataso ta haifi Aayaan ba, taso ta haifi mace ne saboda asa mata sunan biyuninta wato maman SARFRAZ.. dayake Ni sunan mahaifiyar daddynmu aka samini..... In faɗa Miki sanda ta haifi Aayaan har kuka tayi wai ita taso ace mace ta haifa, shiyasa zakiji wani zubin Aayaan yana cewa muda ba'a sommu tunda munzo a maza, to yaza muyi tunda kaddara ta riga fata. To daddyn mune ya bashi labarin yadda Mummy tayi bayan ta haife shi kafin ya rasu ... Kuma har yau har gobe Mummy bata dena ƙulafucin ƴa mace ba Sai dai yanzu taci burine akan matar Aayaan.... Gaban Nawaz ne yayi wata irin faɗuwa amma saita danne bata nunawa Aseey ba. Cigaba Aseey tayi da magana " kuma sis kullum banada addu'ar data wuce Allah yaba Aayaan mata ta gari wadda zamu haɗu mu rufawa juna asiri, saboda Al'amurran duniyar nan sun gama lalacewa, tsorona kada yaje ya auri wadda zatasa ya manta damu, Wallahi idan haka ta faru bazamu iya juraba musamman mummy. Kama mata hannu Nawaz tayi "I'm sorry sis insha'Allah Nima zan tayaki da addu'a, kuma kisa a ranki kamar ya samu mace ta gari ya gama, Aayaan mutumin kirki ne Nima na shaida hakan saboda bai Sanni ba kuma bai taba ganina ba amma ya zage damtse Saida ya taimakamin iya karfinshi. . Murmushi Aseey tayi sannan ta raya a zuciyarta " hmm Nawaz manya ai Aayaan ya riga da ya samu mace ta gari tunda ya rigada ya sameki a Matsayin matar Aure, domin na lura ke din mutumce mai halayen kwarai. Amma a fili sai tace "Ameen sis Nagode sosai sosai da nuna damuwarki a kaina.. "Babu komai, what are friends for? And what are sisters for? Cewar Nawaz tana murmushi "Sis Nawaz kinsan waye asalin Aayaan kuwa? Labarinshi ba kamar na kowa bane, Ni kaina danake yayarshi labarinshi yana bani mamaki. Girgiza kai Nawaz tayi sannan tace "A'a sis bansan labarinshiba.... Gyaran murya Aseey tayi sannan ta fara magana "Aayaan ya kasance yaro mai ƙarfi da kuma hazaka kuma ya kasance duk abinda yasa a gaba saiya iyashi koda kuwa zaisha wahalar da bai taɓa shan irin taba, Sannan gashi wani irin muskilin mutum ne, domin idan aka cire mum da Ni babu mai ganin dariyar shi. Tun yana ƙaramin yaro yake haɗa abubuwan ban mamaki, wani zubin muna barci da dare Ashe shi yanachan yana haɗa mota da kwali kuma yayi mata wiring kuma kiga tana tafiya idan akasa battery, haka wani lokaci har jirgi ya taɓa haɗawa kuma wallahi ya tashi sama ... Ɗaga Kai Nawaz tayi alamun ban mamaki. Sannan Aseey taci gaba "ke in takaice Miki magana har Aayaan ya gama makaranta be taɓa daukar position din daya wuce na ɗaya kona biyuba daga islamiyya har boko. Inda akaso asamu Matsala shine sanda muka gama SSCE Daddynmu yace zaikai Aayaan soja, jin hakan ba ƙaramin tashin hankali bane a gurin Aayaan sakamakon shi anashi yanasone ya zama Medical doctor, wai yanaso ya riƙa taimakawa mutane sosai, wai zai buɗe asibitin kanshi kuma free duk wanda yazo aka dubashi kada a amshi kuɗi... Har ciwo Saida Aayaan yayi, to dayake sunada goodtime da Daddy sai Daddy ya hakura ya samar mishi Oxford University England inda anan yayi 8years yana karantar health issues. To bayan ya dawo ne bada jimawaba Allah yayiwa daddynmu rasuwa... Aayann yayi kuka yayi kuka, yadda kikasan zai haukace, Anan nema ya riƙa nadamar cewa meyasa be yarda yayi soldier ba kodon ya cikawa daddy burinshi... To fa Anan ne zance ya sauya, Aayaan da kanshi ya shirya yaje ya samu aminin dadynmu wato colonel yayi mishi bayanin cewa yanaso ya zama cikakken soldier wanda duniya zata amfana dashi bawai iya Nigeria kaɗai ba.. Colonel yaji daɗi ainun, domin sunada buƙatar sojoji irin Aayaan duba da ƙirar da Allah ya mishi ta jarumtaka da gwarzontaka ga zuciyarshi babu tsoro a cikinta sam. To anan ne colonel ya daukeshi ya kaishi tent ɗin da ake yiwa soldiers training na ƙasa da ƙasa wato international soldiers training forum... Saida mukayi shekara uku bamusa Aayaan a idon muba, mummy har kuka takeyi, nice dai nake karfafa ta Wani zubin dukda cewa Nima tawa zuciyar a karye take .. Bamu tashi Ganin Aayaan ba sai a BBC ana hira tare dashi da Colonel, cewa wai Aayaan yazama cikakke kuma babban sojan ƙasa da ƙasa, kuma ba a iya nan ba, air force da navy duka zai iya shiga cikinsu ayi yaƙi dashi idan hakan ta taso... Yanzu dai in takaice Miki magana babu sojan da gaba ɗaya duniya take so kuma take alfahari dashiba kamar ƙanina AAYAANN, Ni kaina idan na tuna cewa Aayaan ƙanina ne har wani daɗi ne yake ziyartan zuciyata.... Kuma abinda zai baki mamaki game da Aayaan shine muskilancin shi bai taɓa bari yayi budurwaba, duk da kullum yanmata tururuwar zuwa mishi da tasu soyayyar suke Amma akwai wata yarinya sanda muna Oxford taso ta samu cikin bala'in rayuwa.... Domin zuwa tayi ta haɗa baki da likitan Aayaan akan yayi mishi allurar desire inda dole ya kwanta da ita, wai ita kawai so take Taga ta haifi yaro me kama da Aayaan... To Allah shi kadai ya iya kare bawanshi, domin Saida likitan yayi mishi allurar, ita kuma yarinyar Saida ta tabbatar allurar ta fara aiki a jikinshi sannan taje dakinshi ba tare da ko ɗan kamfai ba amma Aayaan ko kallon yarinyarnan beyiba, inda daga karshema dukan tsiya yayi mata ya jefota waje, kuma ta cikin jikinshi shi kadai yasan azabar da yake sha. "Nawaz Ya kamata na barki haka ki kwanta, zuwa wani lokaci zancigaba da baki labarin ahalinmu insha Allah... Murmushi Nawaz tayi, Sannan ta mike ta shiga bayi ta ɗauro Alwala tazo ta kwanta bayan tayi addu'ar kwanciya barci kamar yadda Annabinmu ya umarce mu dayi.... Sai dai sam barci yaƙi zuwa idon ta, illa zuciyarta da take ta nanata mata Tarihin Rayuwar Aayaan, tana mamakin wane irin mutum ne shi. Sai da dare ya tsala sosai Allah ya taimaketa barawon ruhin kowa ya lallaɓo ya saceta yayi gaba da ita. Rashin barcin da basuyi da wuriba yasa basu tashi da wuriba... Tun da asubar fari Aayaan ya fito Cikin shirin kayan sojoji rataye da luggage ɗin shi wadda ita ma da yadin sojoji aka ɗinka ta. Gurin su Mummy ya karasa ya gaida su Sannan yayi musu bankwana, kuma ya shaida musu cewa bazashi da Nawaz ba Saboda tace batason zuwa, sai dai idan yaje yasan bayanin dazaiyi musu game da Rashin zuwan nata.... Mummy taji daɗin hakan sosai barin dama suma sun riga da sun yanke cewa baza'a je da itaba tunda yanzu tayi aure... Sun gama komai amma Aayaan ya kasa tafiya, yanaso koda bazata Kula shiba ya ganta. Tsaff Mummy ta gane me Aayaan yake nufi amma sai tayi banza dashi, mummyn Sarfraz ce tace kaje ɗaki kuyi sallama yau basu tashi da wuri ba. Da sauri Aayaan ya mike yana murmushi sannan ya wuce dakin su Aseey, Dukansu barci sukeyi hani'an, tsayawa yayi ya kare mata kallo tanata barci peacefully baby face ɗinta tayi lufluf da kwabtaccen gashi. Kasa tashinta yayi saboda bayason ya katse mata barcinta, kuma yasan ma ba Lallai ta kulashiba duba da yadda suka rabu jiya. Har yakai bakin kofa ya dawo ya sumbaci goshinta sannan ya fito da wayarshi ya dauke ta photo ya maida ita aljihu.. Koda ya fita harabar gidan anan ya tarar duka bodyguards dinshi sun shirya shi kadai suke jira,. To Aayann Allah ya tsare hanya .. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 42* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Be jima da fitaba Nawaz ta tashi, lokacin har gari ya fara haske, da sauri ta tashi Aseey Sannan ta shige bayi don yin Alwala. Bayan tayi sallar ne tayi azkhar ɗin data sabayi bayan kowace sallar asuba sannan ta miƙe ta nufi kitchen don ɗora breakfast domin ta lura Aseey mayyar barcin safe ce saboda tana idar da Sallah ta koma ta kwanta Ita kuma anata gurin tana ganin abin kunya ne ace akwaisu agidan sannan ace wai sai mummy ta shiga kitchen. Ba wani abu tayi mai wahala ba, illa dai tayi French toast sai ruwan tea data dafa me haɗe da Na'a na'a da citta da kanumfari da dai sauran kayan kamshi masu kara lafiya da kuzari da kuma ɗanɗano a baki. Koda ta gama sai ta shirya a dining Sannan ta koma ɗaki tayi wanka ta shirya, ɗan kishingiɗa tayi da nufin taɗan huta kafin muhsien ya tashi tayi mishi wanka, aikuwa ba ita ta tashi ba sai wajen ƙarfe sha-ɗaya da wasu mintina. Sosai tayi mamakin wane irin Barci tayi haka? Kallon Aseey wacce ke gefe tanayi mata dariya tayi "sis meyasa baki tasheniba? Dariya Aseey tayi "haba ke kuwa! Nifa na hanaki barci jiya da dare, idan ban bari kin ramaba zunubi kikeso na dauka? "Haba sister wane zunubi kuma? Kin manta ke yayatace? Dariya Aseey tayi"to shikenan yanzu dai ki tashi kije kiyi break fast, kowa ya karya amma keda kika dafa baki karyaba. Miƙewa Nawaz tayi tana murmushi sannan ta fita falour, a nan ta tarar dasu Mummyn SARFRAZ Da Mummyn Aayaan suna zaune suna hira. Har ƙasa ta tsuguna ta gaishesu Sannan ta miƙe cike da kunya tayi dinning area ɗin. Tana wucewa Mummyn SARFRAZ tace "Wallahi Nawaz tana burgeni matuƙa, yarinyar Akwai hankali ga sanin ya kamata, sannan ga kunya Wallahi sosai da mutunta na gaba da ita, gaskiya kinyi dacen surukar da ake burin samun irinta koda da kuɗi ne. Ajiyar zuciya Mummyn Aayaan tayi "gaskiya yarinyar Akwai tarbiyya sosai a tare da ita, kuma addini ya kama jikinta sosai... Nan dai sukayi ta tattaunawa gameda Nawaz ɗin har ta gama karyawa, gabansu ta karasa ta duƙa har kasa Sannan tace " Mummy yau me za'a dafa naga Rana ta fara yi. Murmushi Mummyn sarfraz tayi "A'a daughter yau ki huta gaskiya, tunda kikazo fa kike hidimar yi mana girki. "A'a mum babu wata hidima Wallahi, ai girki ba komai bane a gurin mace, Ni daɗi ma nakeji idan inayin girki saboda banaso na zauna tunani ya dameni.. Ƙin yarda mummy tayi Saida Nawaz ta dage tukuna suka haƙura suka barta. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sosai Aayaann yake jin kewa ta kamashi domin tunda ya fito ya barta tana barci fuskarta keyi mishi gizo, ya rasa wace irin soyayyah ce ta kamashi Lokaci guda, duk sai yake jinshi a takure, tafiyar ma ta fitar mishi a rai ba kamar sanda yake ɗokin zuwaba da Farko. Tsaki yayi Sannan yasa hannunshi a aljihu ya ciro wayarshi don ya ɗan daddanna koya rage lokaci, yana danna wa sleeping face ɗin Nawaz tayi mishi welcome, shiru yayi sosai ya maida hankalinshi wajen kallon photon, photon yayi kyau sosai Domin fuskarta very calm tana barcinta peacefully. Samun kanshi yayi da yin murmushi Sannan ya furta "Sleeping beauty!!! Hannu yasa ya shafi pink lips dinta sai kuma ya kashe hasken wayar ya jingina da jikin kujera yana fatan ta soshi kamar yadda yakesonta koma rabin haka, domin yanasone suyi tsabtatacciyar soyayya wadda babu ɓoye ɓoye a cikinta, shidai a nashi ɓangaren baya tunanin Akwai Abinda Zai iya ɓoyewa Nawaz kuma haka yake fatan itama ta daukeshi nan bada daɗewa ba.. Ya ɗan daɗe a kishingiɗe yana tunanin "shin anya kuwa zai iya jurewa ba tare daya fallasa kanshiba har zuwa wa'adin da Mummy ta ɗibar mishiba? Ɗan tsaki yayi yana buɗe idonshi wadanda suka chanza kala Saboda daɗewar da suka yi a rufe, mamaki abin ya bashi Ganin har sun shiga cikin garin Abuja.. Yan mintoci ƙadan ya daukesu suka karasa comprence hall ɗin, sosai mutane sun cika gurin daga yan siyasa sai ƴan sanda da sojoji da mashahuran ƴan boko da masu hannu da shuni... Tunda ya sauka ake sara mishi, yan jarida kuma sai suka maida akalarsu kanshi, kowa burinshi ya ɗauke shi photo domin sunji cewa da taimakon shi aka kama yan ta'addan... Ganin an chukurkuɗe hanyar an hanashi wucewa yasa bodyguards dinshi suka matso sosai suna buɗa mishi hanya har ya samu ya shiga Asalin inda ake taron. Sosai hankaki kowa ya dawo kanshi inda ko zama ba'a bari yayi ba speaker ya miƙa mishi mic, Barka da zuwa yayiwa kowa sannan yayi yan bayanan da zaiyi daga karshe kuma ya bada uzurin cewa Nawaz bata samu damar zuwaba saboda tayi aure kuma mijin yace bai bada iziniba. Sosai mutane basu ji daɗin hakan ba musamman ƴan jarida da suke so su samu kuɗi ta hanyar daukar photunan ta. Maidawa speaker ɗin mic yayi Sannan ya samu guri ya zauna tare da ɗaukar bottle water ɗin dake ajiye a gabanshi yana korawa, shiru hall ɗin yayi ba'a jin komai sai ƙus-ƙus ɗin mutane suna muhawara. Shidai zaune yake kawai amma Sam bayajin daɗin garin, shi a nashi da so samu ne ya koma yau basai yayi wasu kwana uku ba. Speaker ne ya Fara magana "we need your attention here" Sosai kowa ya Dena magana ya maida hankalinshi gurinshi, "To bisa abinda ya faru an yanke hukuncin za'a ba Captain Aayaan Muhammad mai goro duk wani abu da aka yiwa yarinyar Alkawari, an wakilta shi ya kaimata tunda shi yasan inda zai sameta kuma Munsan cewa abinda muka bashi zai isa gurin Wadda akeso ya isa cikin aminci, domin kaf cikinmu babu wanda bai san Aayaann ba. Tafi aka fara, inda daga bisani aka kira colonel aka karrama shi sannan aka kira Aayaan shima aka karrama shi, haka dai akayita yi har zuwa inda aka ƙaddamar da kayan ciye-ciye da shaye-shaye kala-kala. Ganin komai yaɗan lafa yasa Aayaan ya miƙe ya fita zuwa bayan ɗakin taron, tsayuwa yayi yai shiru yana tunani, sosai yayi zurfi a tunanin yaji hannun mutum ya dafa mishi kafaɗa. Colonel ne tsaye a gefenshi yana yi mishi murmushi "Son meke faruwa? Gaisheshi Aayaan yayi haɗe dayi mishi ya bayan haduwa ya su mummy Sannan yayi shiru be kuma yin magana ba. "Son i said what is wrong with u? Dan murmushi Aayaan yayi "Sir i am just not feeling well! Murmushin manya Colonel yayi "Aayaan kenan ba iya shi bane na sanka sosai fa, dole akwai wani abu bayan shi, but zamuyi magana bayan munje gida amma pls kafin nan kayi ƙoƙarin cirewa ranka damuwa, domin har fuskarka Saida ta nuna hakan. Murmushi Aayaan yayi Tare Da cewa "Insha'Allah " Sannan suka dauki hanyar komawa cikin hall ɗin.. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ko bayan Nawaz ta gama abincin saita wuce bayi tayi wanka, hakanan ta samu kanta da son yin light make-up, doguwar rigar Atampa ta ɗauko tasa Sannan ta samu ƙaramin mayafi wanda kalarshi ta shiga da atampar ta yana akanta. Falour ta fita inda suka zauna tare suka ci abinci, sosai Aseey ke janta da hira hakan yasa har sun fara shakuwa da juna. Mummyn AAYAAN da Mummyn SARFRAZ Sun zama kamar tagwaye, duk inda kaga ɗaya to lallai zakaga ɗaya, haka suke yini hira. Aseey ce ta Kalli mummy tace "Mummy don Allah sister Nawaz nakeso ta rakani inga gari" Harara mummy ta balla mata "lallai Aseey so kikeyi Aayaan ya ƙare min tanadi Koh? To wallahi babu inda zakuje. Mummyn SARFRAZ itama cewa tayi"gaskiya ku hakura kawai. Gaban Nawaz ne ya faɗi, domin sam ita tama manta yau bataga koda gilmawar Aayaan ba, shiru tayi tana tunani domin itadai tunda suka zo gidan bata taɓa kaiwa koda karfe goma ba face sun haɗu sau yafi a ƙirga, amma yau kusan ƙarfe uku amma shiru. Duk saita jita wani iri tana tunanin Allah yasa lafiya, gashi bazata iya tambayar kowa shiba, haka gaba daya yinin ranar a falour tayishi saboda tanaso tasan meya faru amma har kusan karfe goma na dare babu Aayaan babu dalilinshi kuma bataga alamun damuwa a tattare dasu ba, lallai kam ashe mutum koh faɗa kukeyi dashi watana saikayi kewarshi idan baka ganshiba. Hakanan ta kwanta namma Saida takai kusan awa biyu bata rintsaba, haka dai har zuwa barcin yazo ya dauketa yayi gaba da ita. Haka Aayaan sosai yake kewar gida, yanaso ya ganta koda hararar shi zatayi, yanaso yaji muryarta koda bashi zatayiwa maganaba. Duk tsayin daren haka Aayaann yayi shi ido farai, babu koda guntun barci daya daukeshi, shi kanshi abin ya bashi mamaki, be taɓa tunanin soyayyar da yake yiwa Nawaz har takai hakanma. Washe gari haka ya tashi wani iri bawai don barcin da baiyiba a'a sai don tunanin daya kwana yi, ya saba da rashin barci Saboda wani zubin har kusan kwana uku yakeyi beyi barciba idan suna filin daga🫣. Dayake a gidan colonel ya kwana, suma yaran Colonel da matarshi Saida suka tambayi colonel ɗin wai me yake damun Aayaan ne? Saboda ya saba idan yazo haka zaiyita tuna yaran wasa yana basu labarai, amma wannan karan ko dinner beyiba ya tafi ɗakin daya saba sauka ya rufe kofa. Koda garin ya waye babu abinda ya sauya, domin Aayaan jin wani irin ƙunci yakeyi ya cika mishi zuciya, duk sai ƴan muskilancin nashi suka dawo suka maida mishi hular sarauta, Be cewa kowa ƙala, ko colonel ne yamishi magana sai dai ya ɗaga mishi gira ko ya girgiza kai. Colonel ɗin be damuba kasancewar yasan halin Aayaan ciki da bai, gefe ya jashi suka zauna yasa aka kawo musu Black tea saboda yasan shine favourite ɗin Aayaan. "My son please ka faɗamin meke damunka? Abin yayi worst ban sanka da irin wannan ɗabi'ar ba sam! Ɗago da kai Aayaann yayi yana tunanin me zai cewa colonel, domin gaba ɗaya bakinshi yayi nauyi kuma yana tunanin ta ina zai soma cewa ya auri Nawaz kuma tunaninta ne ya hanashi saƙat. "Sir banida lafiya ne, and is serious saboda ko barci bana iyayi and kuma damuwa ta isheni, burina kawai naga na koma gida. Murmushi colonel yayi " Son kullum burina inga kayi aure kaima kana tare da naka iyalin, amma hakan yaci tura, bansan meyasa bakason yin aureba! Shekarunka sunkai ace kana da yaro ma ko yarinya but you're still single, yanzu wannan damuwarma da kake ciki waya sanima ko harda matsalar rashin mace kusa dakai, shifa Aure Rahma ne, idan Kanada mata duk damuwar daka shiga zaka faɗa mata kuma zata baka Shawara ko ta tayaka Neman mafita, nidai Aayaan nagaji pls kayi aure na roƙe ka. Tabbas Maganar colonel Gaskiya ce, Ni ɗin ma ai saboda tawa matar na damu, amma Ni matsala ta guda biyu ce, ya za'ayi Nawaz ta yarda da zancen aurenmu kuma tasoni batare da taga anyi mata karfa karfa ba? Na biyu mummy bazata bari na ɗauketa zuwa wata ƙasar ba, balle ƙila idan munje mu saba sosai da ita, ta gindaya min sharadin sai dai Nawaz ta zauna a gabanta har zuwa lokacin da ya dace tasan cewa nine mijinta. Duk acikin ƴan sakwanni yayi wannan tunanin. Dafashi da colonel yayine ya dawo dashi daga nisan kiwon da yayi "my son zan fita Amma pls zanso kafin na dawo ka warware.. Murmushin ƙarfin hali Aayaan yayi "Yes Sir Insha'Allah, amma meyasa bazanyi accompany dinkaba? Murmushi colonel yayi "No Aayaan bakajin Dadi, just saina dawo. Ko bayan colonel ɗin ya tafi Aayaan be tashi a gurin ba sai kawai ya ciro wayarshi ya zubawa photon Nawaz ido "ko yanzu tana ina? Me take yi? Ta nemeshi? Tayi kewarshi kamar yadda yayi Tata? Duk bashida wannan amsar. Tunawa yayi da wayar da y siya mata ranar da sukaje chicken republic, ai kuwa take yaji wani irin farin ciki ya lullubeshi, nuno number yai sai yayi dialling, amma abin haushi is switch off. Kuma shi ya rasa meyasa Aseey da mumy suke mishi haka, ya kirasu yafi sau a ƙirga amma babu wanda yayi mishi Maganar Nawaz, kuma ko muryarta bejiba alamun batama kusa dasu.. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Itama yinin ranar haka take sukuku da ita, amma su Mummy basu ganeba Kasancewar dama ba wani sakin jiki takeyi sosai dasuba, ita kuma Aseey koda taga Nawaz ɗin ta kuma zama so cool itama bata kawo komaiba sai ta ajiye hakan a matsayin kotanaso ta koma gida ne... Mamaki abin yakeba Nawaz sosai, ace babu Aayaan babu alamun shi kuma ko dai dai da rana ɗaya Babu wanda yayi maganar shi, kokwonto ta farayi tana cewa ko dai sun gane Bama shirine? Kada fa suma su tsaneni saboda banason Aayaan. Tsoro ne yaɗan kamata "inaga fa hakane shiyasa yatafi be mini Sallama ba, kuma suma basu faɗamin ba. Kwalla ce ta cikawa Nawaz ido "Wallahi Ni Ban tsane shiba, kuma Wallahi bana ƙinshi, kawai Ni taɓa min jikin da yakeyine banaso... Haka da daɗe zaune tana takanta wasikar jaki, idan ta gama wannan ta ɗauko wannan... Lokaci ne yayi nisa bata saniba.... Hakanan taji tanaso tayi magana da umminta kila ta samu sauki a zuciyarta, to amma tana tunanin taya zata ce Aseey ta kira mata ita bayan suna kallonta a wadda ta tsani ƙaninta. Cikin azama ta miƙe tunawa da tayi da wayar da Aayaan ya siyan mata, aikuwa jikinta har rawa yake yi sanda take kunna wayar, bayan ta kunna ne ta rubuta number umminta tayi dialling, ai kuwa ƙara biyu ta daga da sallama. Jin sallamar ummin sai ya ƙara karya wa Nawaz zuciya ta fashe da kuka, tachan ɓangaren ummi ta fara magana cike da damuwa "Nawaz faɗamin me akayi Miki? Sun faɗa Miki wata magana ne data bata Miki Rai? Ko Wani abunne ya faru? Cikin Muryar kuka Nawaz tace "umminaa don Allah kisa baki Adawo dani gida Wallahi na gaji da zaman nan, ke kawai nakeso na gani. Ajiyar zuciya ummin tayi "akwai wata Matsala ne ko akwai wani abu da suke yi Miki? "Ummi babu wata matsala Wallahi suna sona kuma suna kaunata fiye da zato, kowa burinshi ya kyautata mun, amma Ni kawai nagaji ne kuma ke nakeso na gani... Sosai ummin Nawaz taji daɗi jin ɗiyarta tana cikin kwanciyar hankali, har Saida murmushi ya kufce mata "to Nawaz abinda nakeso dake Yanzu kiyi hakuri, saura kwanaki ƙalilan komai ya daidaita. "To ummi shikenan nagode, yasu amma da kawu? "Duk suna lafiya" cewar umma Sai ta kuma cewa "Nawaz don Allah nasanki da ladabi da kunya da kawaici da son Duk Wanda ya raɓe ki, to don Allah kici gaba a haka koda wasa ban yarda kiyi wani abu dazai ɓatamusu Raiba, Mutanen nan ƴan halal ne, musamman Aayaan wallhi Yaron kirkine bakiga abinda yayi mana ba, sai kinzo mamaki zai kamaki. " Ummi Aayaan ɗin yazo nan ne? "A'a ba kuna tareba? Ummi tace Cikin mamaki "Ummi Bama tare kuma tun shekaran jiya da dare ban kuma ganinshiba. "To wannan wayar waye kika kirani da ita? "Shi ya siyan mini rannan da muka fita, Nawaz tace cike da kwarin gwuiwa. "Allah sarki Wallahi yaron Akwai hankali, to me zai hana idan mun gama waya yanzu sai ki kirashi kiji ko lafiya! "Ummi banida numbershi fa. ''ki amsa gun mummy mana yanzu idan mun kashe wayar.. "To" Nawaz tace haɗe da cewa ummi Don Allah kice ina gaida baffa da amma da kawu... Haka dai suka gama magana sukayi Sallama. Ajiyar zuciya me nauyi Nawaz ta sauke "ummi batasan meyake faruwa bane shiyasa zatace na amshi numbershi, cigaba da danna wayar tayi, ta shiga nan ta fita nan, aikuwa saita shiga contact gwalalo Ido Nawaz tayi ganin wata number anyi saving ɗinta ta "Aayaan your husband" Shiru tayi tana tunanin Lallai Aayaan Akwai ƙarfin hali, ko yaushe yayi saving ɗin number Oho. Tunani ta fara yi akan ta kirashine ko kuma ta share? To idan ta kirashi ma me zata ce mishi? Wata zuciyar ce tace mata kiyi text message kawai, aikuwa sai yaji tayi na'am da hakan, message ta shiga ta fara rubutu kamar haka ```ASSALAMU ALAIKUM``` ```Barka da war haka! Fatan kana cikin ƙoshin lafiya, ban san wane laifi nayiba da har yasa kayi tafiya ba tare da munyi sallama ba, sannan kowa be faɗa minba, babu wanda ya taɓa yimin maganarka...``` ```ina fatan a duk inda kake ka kasance cikin aminci da farinciki, abokiyar faɗan ka Nawaz``` Sai bayan ta tura kuma taji wata fargaba ta kamata, "to idan ya kirata kuma me zata ce mishi? Sai kawai tayi sauri ta kashe wayar .... Aayaann yana zaune yaji ƙarar shigowar message, be damu daya duba ba domin ba wannan bane a gabanshi, shi yanzu damuwar shi taya zaiji daga gurin Nawaz... Miƙewa yayi da nufin ya shiga ciki ya watsa ruwa, daukar wayar yayi ya duba Lokaci ai kuwa idonshi yayi tozali da number da yayi saving da hayaahtih ta turo message, ba shiri ya danna, yama ƙosa ya karanta abinda message ɗin ya ƙunsa, aikuwa yana gama karantawa ya daka wani irin uban tsalle tare da rungume wayar "Alhamdulillah! That means itama ta fara damuwa dani, kenan zata soni, ya Rahman, ya Rabb Nagode, Nagode....... Dialling ɗin number yayi amma bisa rashin Sa'a sai aka ce switch off, hakan ya kara mishi zaƙuwa akan ya koma gida dukda yanzu kashi tamanin da Biyar na damuwar ya nemeta ya rasa, ai kuwa idan ya koma ko me Nawaz zatayi wallahi saiya rungumeta na minti biyar, ai yaci a tausaya mai, cikin gida ya shiga ya cewa su Naufal (yaran Colonel) su shirya zai kaisu shopping inda shi kuma ya wuce gefenshi ya faɗa bayi yanata murmushi.... So yake yaje ya jidowa Nawaz kaya a mall ɗin idan sun fita...... *_~"GASHI NA MUKU DA YAWA SABODA KWANA BIYU BANYIBA, KUMA DUBADA ABINDA YA FARU BA LALLAI KU RIKA SAMUN UPDATE KULLUM BA, MASU BINA PRIVATE DA MASU YIMIN JAJE A GROUPS NAGODE SOSAI ALLAH YA BAR KAUNA."~_* *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 43* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Sosai Hassu take fama da SARFRAZ, domin abin nashi ma kamar ƙara gaba yakeyi, don a halin yanzuma mummy yake cewa Hassu. Kuma kullum sai dai ya kwanta a cinyarta, tun bandi na hanawa har ya gaji ya Dena. Zaune Hassu take ta Miƙe kafa sarfraz yana kwance a cinyarta, ita kuma tana Amfani da metilated Spirit tana wanke mishi ciwo, shikuwa sai raki yakeyi akan idan bata denaba babu ruwan shi da ita, kuma bazai sammata biscuits din Shiba idan bandi ya siyo mishi. Da sauri bandi yace "a'a sarfraz rabani da shirginku babu ruwana domin Nima ba kyaleni kayiba" Sosai Hassu tayi dariya "babban yaya ayi hakuri muna neman sulhu ne... Haka dai suka cigaba da hirarsu gwanin ban sha'awa Kamar yadda suka saba kullum. Tsintar SARFRAZ sukayi amma Yanzu ya zame musu wani sashi na rayuwa, sun san cewa idan SARFRAZ yaji sauƙi Dole ne ya koma Cikin ahalinshi, to amma yaza suyi tunda ba gida ɗaya suke ba, hassu duk tafi shiga cikin damuwa idan ta tuna cewa wata rana ko tanaso ko bata so dolene su rabu da sarfraz, har hawaye takeyi idan ta tuna hakan.... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sosai Aayaann yayi ƙawalliya sannan ya feshe duka jikinshi da turare, cike da kuzari ya shiga babban falourn Colonel Yana kwalawa su Naufal da fudail kira. Mamakine ya kama Colonel wanda shigowar shi kenan "son what causes the sudden change? Wow gaskiya naji daɗi my real Aayaan is back. Dariya Aayaan yayi "sir ka bari in dawo zan faɗa maka abinda ya faru yanzu zamuje shopping ne dasu fudail. "A lallai! Masha Allah haka nakeso na riƙa ganinka kullum cikin karsashi da kuzari..... Su Naufal ne suka karasa suna murmushi "Auncle mun shirya mutafi. Sallama suka yiwa colonel Sannan suka fita daga faloun zuwa harabar gidan..... Ɗaya daga cikin securities ɗinshi yayiwa magana akan ya tuka su, sannan Dukansu suka shiga baya suka zauna Wayarshi ya ciro yana murmushi sannan ya daɗa buɗe inbox yana fldaɗa karanta message ɗin da Nawaz ta turo mishi, daɗi sosai yakeji, kuma sosai zuciyarsa take ƙara mishi kwarin gwuiwa akanta yanzu. Samun kanshi yayi dayi mata reply da. *_Wa'alaikis salaam matar Aayaan_* *_ina lafiya lau Alhamdulillah kuma kema ina fatan kin yini lafiya, ya Bayan rabuwa?_* *_wato bakima san abinda kika minba ko?_* _*Shikenan babu komai nakusa dawowa, ki tanadar mini tarba me kyau*_ _*Mai sonki ba abokin faɗan kiba AAYAANN*_ Bayan ya tura mata sai murmushi yakeyi, bai ankara ba yaji su fudail suna cewa Uncle "munzo sharaton mall ɗin" Namfa ake yinta! Duk Abinda hannun shi yakai sai dai ya saka a basket, yayi siyayyah ta wuce tsammani, suma su Naufal sai jida sukeyi saboda dama yace musu su zaɓi duk abinda suke so.... Haka aka cika Boot dam da kaya sannan seat din baya shima haka, dole suka koma daya motar securities ɗin da suke binsu a baya domin gurin bazai isaba. Bayan sun koma gida ne Aayaan yasa securities suka kwashi siyayyar su Naufal suka kai musu ɗaki, inda shi kuma yabar nashi a Cikin motar... Sosai colonel yake farinciki domin ya lura Aayaan ya warware sosai, sai dai besan silar warwarewar tashi ba. Kallon Aayaan yayi Sannan yace "Son zo ka zauna a kusa dani! Zamuyi magana. Kusa dashi Aayaann ya ƙarasa ya zauna yana murmushi ba tare da yace Komai ba. "Son kasan cewa munada passing out a N.M.S Nan da kwana biyar? Muskutawa Aayaan yayi Sannan yace "No sir Wallahi ban saniba. "Okay to shikenan yanzu koda an gama meeting ɗinmu bazaka tafiba, ka tsaya saimu tafi tare chan Barack ɗin Koh? Wani Irin saukan aradu ne me kamar guduma ya dirarwa Aayaan a zuciya _ya za'a yi yadda naketa murnar komawa gida ace kuma saina ƙara wasu kwana huɗu a gaba?_ abinda Aayaan ya raya a zuciyarshi kenan. Aikuwa baiyi ƙasa a gwuiwa ba yace "sir gaskiya I can't wait that long" "Amma meyasa? Abinda yasa nace ka tsaya shine saboda naga garinku da nisa sosai bazai yiwu daga komawarka ace zaka kuma ɗauko hanya ka dawo Zaria ba, kuma kaga Zaria hanya ce, ana gamawa saika wuce gida kawai. Murmushi Aayaan yayi "sir na manta ban faɗa maka ba, ai ko wannan zuwan danayi daga Zaria nazo saboda dukanmu nida mummy da Aseey munzo gidan yar uwar mummy ziyara. "Au Masha Allah, to ai Shikenan ma faɗuwa tazo dai dai da zama, yaushe Aseey tazo? "Bayan mun rabu dakai mun tafi gida, inaga washe gari tazo. Gyara zama Colonel yayi "Masha Allah, sunzo lafiya dai ko? Ina muhsien abokina.. Aayann yace "sunzo lafiya, Muhsin ɗan rigima yana can nabarshi da Nawaz. Sai Sannan Colonel ya tuna da zancen Nawaz "Aayaan namanta sam in tambayeka meyasa bakazo da daughter ba, kuma ka bada uzurin ƙarya? "I'm so sorry sir, wallahi Nawaz ɗin ce tace ita bata son zuwa, sai Mummy tace to na kyaleta kawai.... Miƙewa colonel yayi "hakanma yayi, bari na shiga ciki barci ya fara rinjayata saboda kwana biyu ban samun yin barci isasshe.. "Okay Sir goodnight" Aayaan yace shima yana miƙewa. Ɗaki ya shiga ya kwanta, yanajin daɗin cewa ya kusa zuwa yaga hasken rayuwarshi. Numberta yayi dialling amma switch off, murmushi yayi Kasancewar yasan kashe wayar tayi bawai chaji bane babu, kunyar Nawaz tana matuƙar burgeshi shi yasa ma take ƙara shiga mishi rai. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Nawaz ce kwance gefen Aseey da wayarta a hannunta tana jijjuya ta, bayan ta gama shirin kwanciya, Aseey tayi nisa sosai a chatting ɗin da takeyi da baban muhsien, sosai takejin daɗin hirar tasu saboda yana faɗa mata yanda yayi missing ɗinta, shiyasa ma yau basuyi hira da Nawaz ba. Shahada Nawaz tayi ta kunna wayar tana salati a cikin zuciyarta. Aikuwa wayar na gama booting message ɗin Aayaan ya shigo, ta daɗe tana wasi-wasi akan ta buɗe ne ko ta barshi. Zuciyar budewar ta rinjayi ta bari, ai kuwa cikin sanyin jiki ta buɗe message ɗin ta karanta, ɗan murmushi tayi "Ni me zan tanadar mishi? Kuma da alamu dai kamar baya fushi dani. Gyara kwanciyarta tayi barci mai daɗi yayi gaba da ita kasancewar yanzu batada damuwa da yawa illa ta sarfraz, kuma itamma ta fara raguwar mata duba da abin ya fara ɗaukar lokaci. Da safe ta tashi tana tunanin me zatayiwa Aayaan tunda harya faɗa mata zai dawo, amma kuma batason kowa yasan saboda shi tayi, murmushi tayi tunawa da tai ai babu wanda ya faɗa mata ranar da zai dawo kuma babu wanda yasan sunyi waya, don haka kenan kome zatayi babu wanda zaice saboda Aayaan ne.. Ko wanka batayiba ta shiga kitchen ɗin, buɗe freezer tayi tana karantar abubuwan dake ciki.. Kaji ta ɗauka guda uku sai kwai da naman Sa, Tana tunanin zatayi dambun naman kaza ne sai tayi mishi meat pie 🥧 saboda rannan da tayi taga yaci da yawa, Sosai Nawaz ta zage tana cire ƙashin jikin kazar bayan ta tafasa ta da kayan kamshi da maggi. Baki buɗe Aseey ta shigo kitchen ɗin "Gaskiya sis zaki koyamin girki Kafin na koma London, yadda zan rikirkita baban muhsien da daɗaɗan abinci kala kala. Murmushi Nawaz tayi batace komaiba sai ma mikowa aseey ɗaya kazar tayi tace "gashi ki tayani cire ƙashin, Sosai suke girkinsu suna hira har suka gama babu wanda ya shigo kitchen ɗin. Ɗaki suka koma sukayi wanka, Aseey ce ta cirowa Nawaz wata Egyptian Abaya a Cikin sababbin kayan zatazo dasu tace tasa, shiru Nawaz tayi tana kintata kuɗin rigar a ranta, domin ko yadin rigar ma abin kallone balle azo kan irin design ɗin da aka danƙara mata a wuya da kirji da hannu, harma bayanta... Sannan aka bisu da swarovski Stones. Cewa tayi "Gaskiya Aunty bazan amsar Miki rigaba don Wallahi da gani wannan rigar mai uban tsada ce, ƙilama innaji kuɗin ta sainayi ciwon kai. Sham mur Aseey tayi sannan tace "Malama cewa nayi ki amsa kisa a jikinki bawai ki zauna kina mini sharhi akan rigarba. Ganin yadda Aseey ta haɗe girar sama data ƙasa yasa Nawaz bata kuma cewa komaiba ta amsa tanata yi mata godiya. Balla mata harara Aseey tayi "kada na sake na kuma baki wani abu ki gode min, wato saboda kin rainani shine Zaki riƙa yimin godiya don saboda na baki Wani abu da bai taka kara ya karya ba. Mamaki abin yaba Nawaz sai kawai ta bata hakuri yayin data koma bedroom ɗin don shiryawa. Sosai Aseey tayi mata kwalliya sannan tayi mata wankan turarukanta, ita kanta Nawaz kamshin turarukan sunyi mata yawa, ga make-up ɗin data zauna ta tsara mata , idan ta kalli mudubi sai taga kamar ba itaba.... Duk ta kasa sukuni gashi kuma ta lura yau Aseey girma ya tashi, dole tabi a sannu.... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Gaba ɗaya Aayaan ji yake kamar ya rufe ido ya ganshi a Zaria, tun asubar fari ya shirya, sosai Colonel yake mamakin wai me ya canza Aayaan hakane? Gashi ba Wani lokaci suka samu wannan zuwan mai tsawo tareba balle ya fahimci wani abuba... Sosai su fudail sukaji Babu daɗi, inda Naufal ma ɗaki ya tafi ya rufe kanshi yana kuka. Shima a ranshi Saida yaji kewa dukda ƙaguwar da yayi akan ya koma gida ɗin.... tun bakwai suka ɗauki hanya...... Sosai suke tafiya, kuma kasancewar safiyace sai hakan yasa titin bai riga ya fara haɗa goslow sosai ba, misalin sha-ɗaya ya kira Aseey ya faɗa mata bar sun shigo Kaduna. Ai kuwa babu shiri aseey ta daɗa feshe Nawaz da wasu irin shu'uman turaruka, domin itafa a nata bata ƙi yau ayi komai a gama ba, don ta gaji da wannan nuƙu nuƙun, ace Mutum da matarshi amma yayita kame kame. Sosai ta daɗa gyara mata fuska sannan tace "sister please kije ki haɗa mana smoothie na ayaba dana Apple da straw Berry, "To" Nawaz tace sannan tamike ta fita Aseey na take mata baya, aikuwa tana shiga kitchen ɗin ta cire rolling ɗin da Aseey tayi mata don gaba ɗaya ji tayi ya hanata saƙat. Sosai ta maida hankalinta kan abinda take yi, cubes ɗin ƙankara ta ɗibo da fruit ɗin da zatayi Amfani dasu ta zuba a bow tana gyarawa. Dai dai nan kuma *_CAPTAIN AAYAAN MUHAMMAD MAI GORO (INTERNATIONAL SOLDIER)_* Yayi landing a harabar gidan su sarfraz, ko tsayawa a buɗe mishi Kofar beyiba kawai ya buɗe ya diro yayi hanyar ƙofar falourn. Ai kuwa yana tura kofar sukayi ido huɗu da Aseey wadda ke zaune tana danna waya. Da gudu ta tawo ta rungume shi tana cewa "yeyy my brother is back! Sosai ya rungumeta shima Sannan ya ɗaga ta sama, dariya takeyi tana cewa "ai ko don saboda dagani sama da kakeyi inaso kayi tafiya, saboda idan ka daga Ni Wallahi abbanmu kake tunamin, Murmushi Aayaan yayi domin shima yasan a gurin Abban nasu ya koya... "Allah ya jikanshi yayi mishi Rahma" Aayaan yace.. Sannan ya kuma Cewa Ina mummy? Cewa tayi "ai su mummy kada ma ka biye ta tasu garama kace ina Nawaz shine ma zaka samu lada, domin tunda ka tafi naga wata irin shakuwa ta shiga tsakaninsu domin cin abinci ne kawai yake fito dasu falour, matarka kuma ta zama kuku batada abinyi sai dafa abinci, infada maka muhsin ma sai yayi mana hijira ya koma gurin su mummy can sasan daddy, kullum fa mu biyune kawai... Murmushi yayi "to ina Nawaz ɗin? Hanyar kitchen Aseey ta kalla Sannan ta Daga mishi gira ɗaya yanda yake yi, Murmushi kawai Aayaan yayi Sannan ya nufi hanyar kitchen ɗin. Muryar Aseey ya jiyo tana cewa "Smoothie take haɗa maka " Daskarewa yayi a bakin Kofar kitchen ɗin, sannan ya bita da kallo yana murmushi.. Ita kuma ta dage sai zuba Apple 🍎 takeyi a blender tana markaɗawa. A babban jug ɗin Glass ta juye smoothie ɗin sannan ta ɗora shi a Saman wani tray me kyau ta ajiye shi a gefe. Tumblers ɗin glass ta ɗauko da nufin ta ɗora a saman tray ɗin. Ɗaga kan da zatayi kawai sai ganin Aayaan tayi jingine da Kofar kitchen ɗin ya zuba hannuwanshi a aljihu yayi crossing kafarshi yana kallonta yana wani irin shu'umin murmushi.. Ai gaba ɗaya tumblers ɗin suka fadi kasa suka fashe, shikuma Aayaan da sauri ya karasa kusa da ita ya ɗaga ta sama sannan yace "meye na tsoron? Kanta ya rankwafo dai dai fuskarshi yana ƙarewa fuskar ta kallo, gaba ɗaya turarukan jikinta sunbi ta duka ƙofofin yancin shi sun ratsa duka jijiyoyin jikinshi... Sauketa ƙasa yayi haɗe da cewa "wane kalar turare kikasa? Banza tayi dashi tana kici kicin kwacewa, murmushi yayi "bazan sakekiba, muje ɗaki ki bani abinda kika tanadar min! Sannan ya ciccibeta yana fitowa daga kitchen ɗin.. Sosai Aseey taji daɗi ganin Aayaann rungume da Nawaz. Cewa tayi "tafi ɗaki kawai zan kawo maka Kayan tarbar ka data haɗa maka..... Zaro ido Nawaz tayi haɗe da cewa "Gaskiya ka sauke Ni" Shi kuma dariya yakeyi yana cewa "ai Aunty Aseey ta rigada ta bada order, sannan ya daɗa rungumeta zuwa cikin ɗakin... A saman gado ya ajiye ta yana rage kayan jikinshi. Ita kuwa Nawaz Abin duniya Ya isheta, gashi Aseey taga ya dauketa amma bata damuba, kuma harda cewa wai su tafi ɗaki... Kwantawa yayi rigingine ya janyo Nawaz ta faɗo jikinshi Sannan ya ƙanƙameta yana cewa i really missed your warmth, kuma Nasha wahalar rashin ki, na kwana uku kawai bakiga yadda na komaba. "Malam kaga ka sakeni wai meye haka ne? Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace " sonkine hakan, and turaren da kikasa is trying to make me crazy... Please give me one kiss. Ganin Nawaz na ƙoƙarin yin kokawa dashi Akan saiya saketa yasa ya maida ta kasanshi ya kuma sakin mata Nauyi Tare Da cewa "idan kin isa yanzu to ki kwaci kanki, sannan ya haɗe bakinsu guri ɗaya yana brushing ɗin lips dinta da Nashi. Dai dai nan Aseey ta shigo "Idan ka gama ga abincin da amaryarka ta haɗa maka nan, Sannan tayi hanyar fita. Tashin hankalin da Nawaz ta shiga bazai misaltuba jin Muryar aseey a Cikin Dakin, it means taga abinda Aayaan yayi Mata kenan. Shikuwa Aayaan murmushi yayi "to bari na gama amsar tanadin da akayi min, sai amaryata tayi feeding ɗina. Sannan ya maida fuskarshi da nufin yimata kiss, Jin zaiyi kissing ɗinta yasa tayi saurin cije duka lebenta da hakoranta yadda bazai yiwu yayi kiss ɗin ba.. Shi kuwa Aayaan dariya yayi "bari na nuna Miki wani salon tunda bakyason wannan, ai kam da sauri Nawaz ta buɗe bakin jin Aayaan na ƙokarin zira hannuwanshi Cikin rigarta... *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 44* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Dariya Aayaan yayi "ai da kin barni kawai, Kinga daga nan duk abinda ya faru ke kika ja. Ita dai Nawaz rufe idonta tayi don bazata iyama wannan al'amarin ba, sosai zuciyarta ke bugawa, domin abin yayi mata nauyi da yawa. _"Wai shikam Aayaan wane irin mutum ne wanda babu kunya sam a tsarinshi, da alamu ma duka familyn su haka suke, tunda ga Aseey tana a matsayin yaya kuma taga abinda yayi amma ta kasa tsawatar mishi"_ Nidai Allah kaga zuciyata ka tseratar dani daga fasikanci, wai me Duniyar ta zama ne? Kowa burinshi yin zina! Harshen Aayaan da taji cikin bakintane ya dawo da ita daga tunanin da takeyi, kissing ɗinta yayi passionately sannan a hankali ya dawo da lips ɗinshi saman goshinta, namma yayi kissing ɗin goshin haɗe da cewa "May Allah bless you my love" rage nauyinshi yayi domin ya lura ko nunfashi daƙyar takeyi. "Zo muje kiyi feeding ɗina" Aayaan yace tare da riƙo hannayen ta yana miƙewa, gaba ɗaya jikinshi yayi weak, harta idonshi sai ya koma kamar yanzu ya tashi daga barci. Kwace hannunta tayi tana cewa "Wallahi sai Allah ya saka wa mijina duk abinda kayi min, domin kai kanka Nasan bazakaso ka auri wacce Wani namijin yayi mata Abinda kake min ba. Kuma Allah idan kayi wasa saina faɗawa Mummy tunda naga abin naka gaba yake yi. Komawa yayi ya danne ta "Okay bari nayi me gaba ɗaya Kinga sai Allah yafi sakawa shi mijin naki dakyau, kuma itama Mummy kyafi jin daɗin faɗa mata! Hannu yasa da nufin ya zuge zip ɗin dake gaban rigar ta, aikuwa da sauri Nawaz ta ƙanƙame zip ɗin tana cewa "Don darajar Annabi kada ka buɗe Min riga, Wallahi na fasa faɗa, kuma ko dama bazan iya faɗa ba nadai ce ne saboda ka rabu Dani. "Nop! Nikuma bazan iya haƙura ba" hannu yasa ya ɗage rigarta ta ƙasa. Nawaz bata ankaraba sai jin _bare hand_ ɗinshi tayi a saman cinyarta, ai take wani irin shock ya ziyarci kwakwalwar ta. Shima ta ɓangaren Aayaann Hakan ne ya faru, domin wani abu yaji tun daga yatsun kafarshi har cikin kwakwalwar shi, a Tare suka sauke nunfashi mai ɗumi. Idon Nawaz duk ya cika da hawaye "yaya Aayaann kaga kai yayanane kuma wallahi ina girmama ka har cikin zuciyata, kuma na baka babban matsayi saboda ta sanadinka nake Raye har zuwa yanzu, don Allah kada ka yarda ruɗin zuciya yasa mu tafka abin kunyar dazai yita bibiyarmu har kabarinmu.... "Sosai Aayaann yaji daɗin maganganun Nawaz, kuma Hakan ya daɗa tabbatar mishi da hankalinta, sannan yasan cewa tana Ganin girmanshi sosai... Cikin raunanniyar murya yace "Nagode sosai, kuma insha Allah zan kiyaye gaba, amma zaki bani abincin? "Eh" Nawaz tace domin ta ƙosa ya ɗaga ta... Aikuwa yana dagata har wani irin ajiyar zuciya tayi tana sauke nunfashi a hankali... Warmers ɗin ya janyo gabanta da plate Sannan ya buɗe, kallonta yayi yace "All this for me? Naji Aseey tace ke kikayi mini, is she telling the truth? "Eh Nina Yi" Nawaz tace cikin ƙosawa, gaba ɗaya ta ƙosa tabar ɗakin ga Wani nauyinshi da takeji bata soma yana kallonta, cewa yayi "Madam pls ayi feeding ɗina mana! "Haba Don Allah, yanzu dambun naman ko meat pie 🥧 ɗin ne zan baka? Bayan kasan cewa basa ciyuwa da cokali Saida hannu! Murmushi yayi "ai dama da hannun nakeso ki bani, amma pls a fara bani smoothie ɗin nasa saboda kamshin shi ya cika min hanci.. Banza tayi dashi ta dauki tumbler ta tsiyaya takai center bakinshi ba tare data ce komai ba. Shima yasan ya matsa mata shiyasa ya kafa bakinshi ba tare da yayi korafi ba, Saida yasha da yawa sannan ta cire yashaƙi iska sannan ta kara mayarwa, bayan ya shanyene ta matso da bowl ɗin wanke hannu ta wanke hannunta a ciki Sannan ta ɗibi dambun naman takai bakinshi, buɗe wa yayi ya amsa amma saiya riƙe hannunta a cikin bakin. Kallonshi tayi "kaga ka sakin mini hannu" "Bakiga na kasa Magana bane, smoothie ɗin ne yayi daɗi da yawa, saikuma da kika ƙara min da dambun naman nan naga bazan iya resisting ba, Gaskiya you are a good cook! Zare hannunta tayi taci gaba da bashi, data lura ya ɗan ci da yawa sai ta dauko meat pie 🥧 guda ɗaya shima ta riƙa bashi a hankali harya cinye.. Bottle water ta buɗe ta kafa mishi a baki, nanma Saida yasha da yawa ta cire mishi ta ajiye sannan ta wanke hannunta. Cewa tayi "iya abinda zan iya baka kenan, amma idan baka ƙoshiba zaka iya ƙarawa.. Janyo hannunta yayi da nufin ta faɗo jikinshi amma saita choge "ya mukayi dakai? "Au na manta I'm sorry, Amma ya akayi kikasan gejin cikina? Sham mur tayi Sannan tace "kintace kawai nayi" "Masha Allah, shiyasa nake ƙara sonki saboda akwai ki da zurfin tunani. Taɓe baki Nawaz tayi "Nidai kaga ɗaki zani" Kallonta Aayaan yayi yana murmushi ƙasa ƙasa don ya gane kunyarsa takeji saboda Sam taƙi Bari su haɗa ido "Nan titi ne kenan? Ɗago ido Nawaz tayi ai kuwa suka haɗa Ido, ɗaga mata gira yayi haɗe da kashe ido ɗaya "yadai? Da sauri ta ɗauke kanta bata kuma Cewa komaiba don ita so take yi su rabu lafiya, amma taga take taken Aayaan bazai barta ba... "Madam i love You! Please Don Allah ko 1% kisoni a cikin 100% danake Miki. Banza tayi dashi, ai kuwa ya miƙe ya koma kusa da ita, riƙe mata hannu yayi "sweet heart Ina magana kinyi shiru meyasa? "Shagwaɓe fuska tayi "Ni nace maka ɗaki zani! Pls ka barni na tafi. "Okay to tashi muje na rakaki" da sauri Nawaz ta miƙe tana jin daɗi cikin ranta, don zata rabu da wahalar Aayaan. Ai kuwa bata ankara ba taji Aayaan yayi wuff ya dauketa, yana dariya. Yaya Aayaann pls ka saukeni don Allah, "bazan sauke kiba saina kaiki falour saboda nina daukoki daga can" Sanin cewa ko me zatayi bazai sauketaba yasa tayi shiru don kada tace Wani abu ya fasa kaita... Buɗe Kofar yayi ya nufi cikin falour yana cewa "I Love You... Pls kema kice You Love Me! A tsakiyar faloun ya sauketa inda Mummyn SARFRAZ Da Mummyn Aayaan ne zaune suna hira, sai Aseey a gefe alamu ya nuna waya takeyi, MUHSIEN kuma yana barci a Saman two sitters couch... Kunya da tashin hankalin da tunda take bata taɓa jin irinshi bane ya kamata, da ace ƙasa zata tsage ta faɗa ciki da hakan yafi mata daɗi fiye da komai. Shikuwa ko a jikinshi sai murmushi yakeyi Sannan yace "sannunku mummies, Sanda na dawo Aunty Aseey tace kuna part ɗin daddy shiyasa ban muku sannu da gida ba... Ita kuma Nawaz yana sakin Mata hannu ta kwasa a guje tayi ɗaki tana haki Kamar wadda ta yini gudu.. Kowa Saida yayi Daria, shikuma Aayaan yaɗan sauke kai yana murmushi, shidai kunyar Nawaz tana bashi sha'awa matuka... Yasan kuma Yanzu Kafin ta bari aganta sai an sha fama.. Balla mishi harara Mummy tayi "wai Aayaann yaushe ka zama mara Kunya kuma mara jin magana ne? Nace maka Babu ruwanka da yarinyar nan har sai randa nida kaina naji na gamsu, amma shine ka cicciɓeta ta karfi da yaji ka tafi da ita, saboda kai ga ILIYA ƊAN MAI ƘARFI ko? Mummyn SARFRAZ ce tace "Don Allah ki rabu dashi mana, wai Duk dokar ta meye haka, Mutum da matarshi, kuma dai yanason kayarshi to meye na sa Miki wasu tsauraran sharuddan da Allah ma besa mishiba? Gaskiya nidai kirabu dashi.. Simi Simi Aayaan ya wuce ya tafi ɗaki, Aseey kam sai dariya takeyi tana toshe baki.... Balla mata harara Mum tayi sannan tace ai Nasan harda haɗin bakin ki, kuma kici gaba tunda duka kun maidani sa'ar ku. Tunda Aayaan ya koma ɗaki yake murmushi, ya kasa yin komai dai ya juya nan ya juya chan akan makeken gadon SARFRAZ... Wayar shi dake cikin aljihun wandon shi ce ta hau ƙara, cirowa yayi don yaga waye... Murmushi yayi ganin Babban abokinshi kuma school, class, and course mate dinshi Wato Farouk , "Assalamu alaikum bross yadai? Ta chan ɓangaren Farouk yace "soja mazan fama! Soja marmari daga nesa...... Ina fatan ba'a Filin yaƙi kake ba dai Koh? "Oh Zaka Fara kenan Koh Farouk? Aayaann yace yana shafa ƙasumbarshi... Da gaske nake akwai Magana ne Wallahi! Farouk yace cikin serious tone..... "Okay to inaji! Ya akayi? Gyaran murya Farouk yayi Sannan yace "dama Akwai wani patient ne da wasu Fulani suka kawo min shi, to lalularshi tayi kama data Shaheed wanda aka Kawo min chase ɗinshi last year. To kuma kaga an kashe maƙudan kudade Kafin ya samu lafiya, kuma su waɗannan da alamun ko kobo basuda ita, shine nace musu zanyi maka magana idan da hali zan kirasu saboda na amshi lambar babansu.... "Ohhhh ayyyah ALLAH Sarki amma dai abin da sauƙi Koh? Eh da sauƙi saboda shi ba hauka yakeyiba sai dai abin nashi yayi kamar wanda yayi loosing ɗin memorinshi ne... "Okay to inaga zuwa next week zamu Shigo garin, zanzo asibitin ayi duk Abinda ya dace sai a shirya fita waje dashi. "Okay to, the billionaire Allah yaja kwana, ALLAH ya jikan baba... AMEEN Aayaan yace Sannan suka ci gaba da hirar su ta matasa..... °°°°°°°° NAWAZ kam tunda ta shiga ɗaki ta kasa zaune ta kasa tsaye, gaba ɗaya zuface take karyo mata duk da sanyin gari da kuma sanyin A.c ɗin dake zagaye dakin.. Shawarar data yanke guda ɗaya itace zata gudu da asuba, domin wannan gagarumin abin Kunyar da Aayaan yasa suka aikata bazai barta ta iya kallon su mummy ba. To masu karatu kunjifa, shin Nawaz zata samu damar guduwa kuwa, sannan Aayaan zai haɗu da SARFRAZ ko kuwa saɓani zasu kuma yi???? Ku biyoni shafi ba gaba don jin Yadda zata kaya.... *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 45* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Haka Nawaz ta yini a ɗaki ko abinci bata ciba, tana tsoron fita falourn saboda kada ta haɗu dasu mumy. Sai da Aseey taga abin dagaske ne sannan ta samu ta dafa mata Noodles ta kawo mata, da kyar Nawaz ta tashi ta amsa, Saboda kwanciya tayi ta rufe da duvet. Aayaan kam yana chan yana fama da muhsien, wai dole sai sunje yawo gashi kuma shi sam bayason fita yau, yanaso yaɗan huta kafin al'asar... Hakanan dai daƙyar ya samu yayi mishi wayau akan zai kaishi gobe, sannan ya zuge back pack dinshi ya kwaso chocolate ya haɗa shi dasu. A Ranar kam kowa Saida jikinshi ya gaya mishi da yunwa, kasancewar dama Nawaz ce keyin girkin sai kowa ya sakankance. Sai wajen ƙarfe biyu da hantsi ya dubi ludayi shine Aseey ta leƙa kitchen ɗin ta dafa Noodles da kwai, haka kowa yaci don sun san mai dafawar bazata fitoba balle su sa ran samun abincinta. Ko bayan da Aseey ta dame ta akan ta tashi taci abincin hakanan ta ɗaure fuska "Aunty a Gaskiya Abinda kikayi baki kyautaba, kinsan dai babu kyau namijin daba muharraminka ba ya riƙa taɓa maka jiki amma kina kallo ya Aayaan yana daukaka kuma a matsayinki na Babba baki tsawatar mishi ba... "I am sorry dear! Bazaki gane komaiba har sai an sanar dake, amma bani keda wannan damar ba sai dai idan zaki tambayi Mummy ita zata feɗe Miki biri har wutsiya. Shiru Nawaz tayi kirjinta kuma na bugun tara-tara, hakanan taji Maganar batayi mata ba ga Wani tsoro daya dirar Mata a zuciya lokaci guda ta zaro ido "Aunty Don girman Allah ki sanar dani koma menene" Murmushi Aseey tayi "ooh! Sisto meye na tada hankalin ki haka? Sekace nace miki gobe zaki mutu! To gaskiya Ni banason wannan tsoron inasone ki zama jaruma. Nawaz Kamar zata zunduma ihu tace "Aunty ba wannan ba don Allah Ni kiyimin bayani ne yadda zan gane me kike nufi" itakam Aseey abinma dariya ya koma bata domin duk Nawaz ta fita daga hankalinta harda ƴar zufarta... Murmushi tayi tace "my sister nothing bad, bafa Wani abu bane kawai dai naji kamar Mummyna tana cewa zataje ta roƙi baffa akan a barmata ke kici gaba da zama tare damu, wai tanajin daɗin zama dake.... Saida Nawaz ta sauke Wata sassanyar ajiyar zuciya Sannan tace "indan wannan ne babu Matsala Insha'Allah lokaci zuwa lokaci zan rika zuwa ina yi mata kwana biyu. Rashin wayon Nawaz Aseey ta gani Saboda Yadda ta yarda da maganar Lokaci guda batare data tuna abinda Aseey ta fara ce mata ba . Bata fuska Nawaz tayi 😞 a gaskiya banji daɗin Abinda yaya Aayaann yayi mini ba, ace a gaban su Mummy ya fito rungume dani Amma shi ko a jikinshi, kuma hmmm bari Kawai nayi shiru tunda babu wani amfanin faɗa domin aikin gama ya riga da ya gama. ° Yau kusan kwana huɗu da dawowar Aayaan Amma Nawaz ta kasa samun damar guduwa, saboda duk sanda ta tashi da asbah sai dai taga Aseey zaune, abin har mamaki yake bata saboda da ita take tashinta amma yanzu sai taga ta rigata tashi, har Saida Nawaz ta Fara tantamar anya ko dai Aseey taji sanda tace zata gudu ne! Ta ɓangaren Aayaann kuma yaune za'a yi passing out a N.M.S barrack ɗin dake sabon Gari a Zaria, inda achan zai haɗu da Mutane kala kala harda waɗan da a ƙalla ya Kai 5years rabon da su haɗu.... Shiryawa yayi sosai a cikin complete New uniform waɗanfa suka bi ingarman jikinshi suka zauna kamar Anan Allah ya halicce su, sosai yayi kyau Sannan ya ɗauko Beret ɗin soldiers ya kafa a kanshi ya ɗan karkata ta gefe abin dai gwanin ban sha'awa sai wanda ya gani... Bai ɗauki komaiba ba illah side pack wadda ya ɗan Zuba abubuwan da zai iya buƙata Tare Da ƙaramar bindiga koda wani abin zai iya faruwa. Duk Cikin kwanaki huɗun sam bai kuma ganin Nawaz ba, abin har Saida ya ɗan taɓa shi Amma ya shanye tunda komene ne ma ai shi yaja. Falour ya fito inda be tarar da kowa ba sai motsi da yaji a kitchen alamun akwai Mutun a ciki.. Kitchen ɗin ya ƙarasa ya leƙa Don ganin ko waye a ciki, ai kuwa Aseey ce ta kuƙe sai yanka cabbage takeyi da carrots. Murmushi yayi "Aunty sannu da aiki! Murmushi itama tayi "yauwa bro harka shirya? "Eh sis" Aayaann yace yana rungumeta, sannan ya ƙara cewa "sis kiyi mini addu'a, Sannan inasu Mummy suma inyi musu sallama? "Suna back yard! Tun ɗazu naga sun fita suda MUHSIEN kasan sai bankwana sukeyi Tunda sukaji cewa gobe zamu koma, Wallahi bakaga ɗazu ba har Saida suka bani tausayi duk sun damu Kamar suyi kuka... Yar dariya Aayaan yayi "nifa amintar Nan tasu har dariya take bani, Ni nakancema ko soyayyar biyunin Mummy ce ta koma kan ɗaya Mummyn? Ita ma Aseey dariya tayi Sannan tace "kila hakane, and Kafin ka tafi ka shiga kuyi sallama da sweety ɗinka Don Nasan Kayi kewarta da yawa. "Ooh Aunty kin Zama Yar sa ido 👀 amma zaku haɗu Ni babu ruwana ... Sakinta yayi yace "to mudai sai Allah ya dawo damu, sannan ya fita daga kitchen ɗin zuwa dakin su Aseey. Yauma dai a kwance ya tarar da ita tana barcinta hani'an, sanye take da pink ɗin girly sleeping dress 👗 half gown ce wadda ta tsaya mata iya cinya, sai hular kanta Wadda itama Pink ce wadda akayita da net amma ta zame zuwa baya inda ta bayyanar da kyakkyawan baƙin gashinta mai santsi, abin gwanin ban sha'awa.. Murmushi yayi yace "sleeping beauty" sannan ya ciro waya ya dauketa photo, mayar da wayar yayi amma ya kasa fita, yanaso ko yayane yau dai yaji duminta tunda Allah ya haɗa su.. Side pack ɗinshi ya ajiye a gefe sannan ya zauna a saman gadon tare da ɗaukar ta kacokan ya ɗora ta a Saman cinyarshi, Cikin Barci Nawaz taji kamar an dauketa Sannan kuma sai turaren Aayaan da yayi Mata sallama a kwakwalwar ta, a hankali ta fara buɗe ido don ganin gaskene ko mafarki, aikuwa bata kai ga budewaba taji yasa hannu ya matsar mata da gashin daya sauko mata a goshinta. Aayaan dake kallon fuskarta sai yaga fatar idonta nayin rawa alamun ta tashi daga barcin, murmushi yayi sannan yace "Sweetheart kin tashi? Saukar muryarshi data jiyone ya ƙara tabbatar mata da cewa lallai ba mafarki takeyiba. Aikuwa da sauri ta buɗe ido tana kallonshi a razane "wai yayaa Aayaan meyasa bazaka rabu dani bane? Mai yasa kake son taɓa min jikine? Nifa gaskiya na gaji Wallahi.... Duk wannan masifar da takeyi Aayaan beji komai ba illa laɓɓanta daya ƙurawa ido sunaa juyawa kamar da gangan take musu hakan. Kanta ya kama ya haɗa bakinsu guri ɗaya ya fara sucking ɗin lips ɗinta, aikuwa Nawaz sumane Kawai batayiba, tashin hankali shock da komaima haka suka sauka a cikin kwakwalwar ta a Tare..... Sosai Aayaann yayi kissing ɗinta Sannan ya saketa yana maida numfashi da sauri da sauri, gaba daya mood ɗinshi ya chanza. Side pack ɗinshi ya buɗe ya ciro wrappers ɗin yan dubu ɗaya guda biyu ya ajiye mata a Saman cinyarta Sannan cikin kasalantarciyar murya mai kama data Mai jin Barci yace "Ni zan tafi Please kiyi mini addu'a, wancan karan haka na tafi bamuyi Sallama ba wallahi har zazzaɓi Saida nayi, hope zakiyita yimin addu'a, kuma Kinga dana dawo bamu samu isasshen lokaci nayi miki bayanin Abinda ya faru a Abuja ba, Sannan kuma sun baki kyaututtuka da yawa, sai tsarabar ki amma duk suna mota saboda naga gobe zamu tafi gida kuma kayan da yawa shiyasa na barsu acan kawai.. ita dai Nawaz tana zaune Kamar Wadda aka dasa, murmushi yayi sannan ya sunkuceta ya ɗaga ta sama yana juyi da ita, ƙasa yayo da ita Sannan ya saita bakinsu ya Kuma bata Wani passionate kiss ɗin... Hugging ɗinta yayi sosai Kamar zai maida Ita Cikin jikinshi Sannan ya ɗora kanshi a Saman kafaɗarta.. Magana Ya fara "i really love you Nawaz, with All my heart, I want to have u as a sister, daughter, mother, Best friend and wife... Don Allah ki soni kema 😭 Wallahi a yanda nakeji sonki Zai iya haukatar dani..... Aseey ce ta buɗe ƙofar tare da cewa "Aayaan Daga cewa zakuyi Sallama shine ka kwashi Tsawon awa ɗaya baka fit........ Maganar ce ta tsaya mata a wuya Ganin Irin rungumar daya yiwa Nawaz. Aayaann ka saketa mana! Kada fa ka ballata, ajiyar zuciya ya sauke Sannan ya saketa tare da ɗaukar side pack ɗinshi Yana fita daga Dakin... Nawaz dai ko motsi ta kasa, haka zalika kwakwalwarta ta Dena aiki har saida taji fitar motar su sannan wata wawiyar ajiyar zuciya ta kufce mata.... Aseey kuwa dama tuni tabi bayan shi ta rakashi gurinsu mummy sukayi Sallama Kafin ya shiga Mota sannan suka tafi. Nawaz dai jikinta take kallo da yololuwar rigar jikinta, Lallai Aayaan ya gama da ita, yanzu haka ya gama ƙare Mata kallo? Sannan be barta Anan ba ya kuma yin kissing ɗinta... Aiko SARFRAZ da yake muna Mata tsaurin ido idan zaiyi mata Abu a ɗari ɗari yakeyi, kuma baya wuce gona da iri, amma ta lura Aayaan hankalinshi kwance yakeyin komai kuma Sam babu ko ƴar kunya... Tana zaune Aseey ta shigo "sis kina zaune har Yanzu, bari na shiga bayi na watsa ruwa sai in fito in kira su mum a garden sai muci abinci. Ci kanki" Nawaz batace ba, ko kallonta ma bata yiba. Aseey na shiga bayi Nawaz ta miƙe ta cire rigar jikinta tasa doguwar riga Sannan ta ɗora hijabi, wayarta ta ɗauka sai dubu biyu data Zara a Cikin kuɗin da Aayaan ya bata tayi hanyar waje cikin sauri. Cikin iKon Allah har ta fita Daga gidan Babu wanda ya ganta, mai keke napep ne yazo wucewa ai kuwa ta tsayar dashi jikinta na rawa ta shiga tare da cewa "malam kaini dogarawa. Har saida taga sun fita daga layin tukuna ta sauke ajiyar zuciya tana lulawa duniyar tunani "naga Idan na zauna mutumin Nan zai iya hakemin inyaso daga baya sai yace ruɗin shedan ne, nikuwa dana zauna wani ya keta Min haddi Gara na gudu wallhi koma menene ya faru na yarda. Sosai ta faɗa Duniyar tunani, tana tunanin taya zata koma gida? Gashi Babu Wani kuɗi a hannunta illa dubi biyun data ɗibo, Tunani ta fara yi akan ina zata inda zaifi safe Yadda ko umminta Kada a faɗa wa, Domin tasan Idan ummi taji to baffa yaji, kuma kenan dole ta koma.... Tsaki tayi ganin Kamar fitowar Tata ma ba nasara.... Danguntun murmushi ne ya kwace mata data tuna da Wata aminiyar Mummy wadda take a hayin ojo commercial. "Driver pls kaini ojo kawai, Abar zancen dogarawar nan,. "to Hajiya" drivern yace tare daci gaba da tukin shi. ° Aayaann kam yana zaune a Mota amma zuciyar shi tana gurin Nawaz, ya rasa meyasa yake yiwa Nawaz Irin Wannan son, sosai yake sonta, kuma zai iya bada komai saboda ya mallaketa... Abubuwan da suka faru yake tunawa yana murmushi "to Yanzu idan Nawaz tasan Ni mijinta ne koya za'a yi, hmm Nasan dai dole asha rigima, Dai dai nan suka isa barrack, koda Aayaan ya fito saiya murtuke fuskarshi Kamar wanda besan ma meye dariyaba, soldiers ne sahu sahu Sai salute sukeyi mishi. Shi kam yana wani ciccijewa, nace Ooh Aayaan a waje ZAKI a gurin Nawaz kuma jinjiri🤣🤣🤣.. Dai dai nan itama Nawaz suka isa kofar gidan aminiyar ummi, sauka tayi ta bashi kudin ya bata chanji sannan ta nufi cikin gidan. A rufe ta tarar da Kofar Dakin matar, ai kuwa Kamar ta zunduma ihu ta fita da sauri Saboda Kada Mai adaidaitar ya tafi, don idan yatafi zata sha wahala kafin ta samu wata, ai kuwa babu shi a gurin sai dai alamun tayar shi.. Wani dan shaye-shaye ne ya fito daga gate ɗin commercial wanda ke baya, Ganin Nawaz da yayi a tsaye ne yasa ya ƙarasa kusa da ita Yana ciccijewa irin yadda yan shaye-shaye sukeyi, haɗe da yin murmushi "ke cika ya akayi ne? Ko kina buƙatar chaji ne? Zaro ido Nawaz tayi Sannan ta Fara dana sanin fitowa daga gida, domin gurin da take ko kasheta yayi Babu wanda zai sani *Wallahi kaina ciwo yake yi, wata me kitso ce tabi da zazzamge mini kai* *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 46* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Ja baya tayi bata Kula shiba, ai kuwa mutuminka sai ya daɗa matsawa kusa da ita "cika ina magana fa amma kin wani shareni" Sosai tsoro ya kama Nawaz Amma bata nuna mishiba saboda kada yaga lagonta... Ɗago kan da zatayi taga inna talatu tana sauka a kan machine. Da gudu ta ƙarasa kusa da ita"inna sannu da zuwa! Na shiga gidan naga dakinki a rufe, Allah ne yayi zamu haɗu... Shima ɗan shaye-shaye sai yayi gaba abinshi ganin inna tazo, dama don ya ganta ita kadai ne.. Murmushi tayi "yarinyata gaskiya naji daɗi sosai dana ganki, yaushe kuka dawo? Umminki batace min ga Ranar da zaku dawoba. Inna talatu tace tana sa key a cikin padlock ɗin tana murɗawa, aikuwa Kofar ta buɗe Sannan duka suka shiga ciki. Bayan Nawaz ta ɗan hutane inna ta kawo mata snacks da drinks donta samu ta ci, bata wani ci da yawa ba saboda zuciyarta na raya mata da kyar Idan inna zata yarda ta Zauna a gurinta ba Tare Da kowa ya sani ba. Ko Bayan ta gama ci inna tace "Nawaz Yanzu kin Dena zuwa gurina, amma da duk ranar juma'a sai kin zo kinyimin week end. "Inna kiyi hakuri Wallahi abubuwa ne sukayi min yawa saboda ko kafin mu tafi chan Maiduguri ɗin na samu aikin koyarwa a makarantar HAYATUL ISLAM" Koda naji! Ai nasanki Akwai Zumunci dole dama akwai abinda ya hanaki zuwa, to ya aikin naki yanzu? Wallahi yanzu banma san a Wane babi nakeba, don ko excuse ma ban amsa a gurin Malam Abdullahi ba nadena zuwa. "Oh Nawaz manya, yaushe Ita ummin naki zatazo? Ko zatazo anjima ne saiku koma tare? To Anan ne Nawaz ta kwashe duka labarinta tun daga kan Ranar da umma ta Turo ayi mata fyaɗe har zuwa yau data gudo daga gidansu Aayaan, Sannan ta ƙara Mata da cewa "kuma inna Gaskiya Ni na kasa gane me Aayaan yake nufi dani, saboda saikiga yanata shishshige min, nikuma banaso gaskiya. Mamaki ne tsububu a idon inna "Lallai ladidi! (tana nufin umma kishiyar ummin Nawaz) "Yanzu har rashin imanin ladidi yakai ta Turo Yan iska suyi miki fyaɗe? To ta Allah ba Tata ba, kuma Wallahi munanan zakiga mummunan matakin dazan dauka a kanta... Dafa Nawaz tayi "kada kiji komai kiyi zamanki anan, "ita Rahma inbanda abinta ai yanzu ne ya kamata ta jaki a jiki saboda ki samu sauƙin abinda kikeji a zuciyarki, amma shine ta sakar wa duniya ke, ba tare data san kosu su waye ba..... "Ki barni da ita saita kirani tana neman ki Ido rufe tukuna zanyi mata tsiya.... Daɗi Nawaz ta riƙa ji akan ta samu ƴanci Yanzu bamai yi mata dole, Spare ɗakin da Nawaz take zama idan tazo mata week end nan ta tafi don dama inna cewa takeyi ɗakin Nawaz ɗin ne, ai kuwa a gyare ɗakin yake tsaff kamar akwai me zama a ciki. Ita kuma inna saita shiga daki ta zauna a bakin gado tana jimamin abinda ya faru, wayarta ta ɗauka ta danna number ummin Nawaz don taji ta bakinta... Ƙara biyu ana Uku ta dauka "Assalamu alaikum Barka da Yamma ƴar Uwar Alkhairi " cewar ummi tachan ɓangaren "Wa'alaikumus salaam masoyiyar kwarai! Wai kam lafiya? Naji kwana biyu wayar ki bata shiga idan na kira? "Lafiya lau Wallahi an ɗan samu matsalar wutar nepa ne, amma an gyara, kuma dama Nima itana neman Yadda zamu haɗu saboda akwai maganganun da nakeso mu tattauna. "Okay to Ina jinki, fatan dai lafiya?" Inna tace tana daɗa gyara zamanta a saman gadon da take zaune... "Kinsan anyi bikin Nawaz kuwa? Kuma Yanzu hakama tana tare dasu amma batasan da hakan ba! 😳😳😳 Zaro ido Inna tayi Babu shiri don kalmar tayi mata nauyi sosai, ya za'ayi ayiwa Mutum Aure ba Tare Da Sanin shiba? "Tsaya ƙawata kidena ma wannan zancen taya za'a yiwa ƴata irin wannan mummunan abin? Ƙasa da murya ummin Nawaz tayi "wallahi dagaske nakeyi, amma matsalar duk daga gurin baffa ta faro, don zuwa yayi sukayi magana da kakan Nawaz ɗin, wato sirikina, Ni kaina Lokacin na shiga tashin hankali mara misaltuwa amma kinsan dai halin baffa kaifi ɗaya ne baya chanza magana.... "Na fahimceki! To amma meyasa ba'a sanar da ita ba? Shiru ummi tayi, sai kuma tace "Nima dai na rasa dalili amma Farko baffane Yace kada a bari ta sani.. Nan dai suka tattauna akan maganar sosai, saidai Koda wasa inna bata furta Cewa Nawaz tana gurintaba.... Ko Bayan da sukayi Sallama kasa tashi inna tayi a inda take "ita dai Nawaz haka tata kaddarar take? Amma Wallahi baffa ya bani mamaki ya za'a yiwa yarinya auren Dole kuma ba Tare Da Sanin taba? Sannan an dauketa an damƙa Musu ba Tare Da anyi Mata wani cikakken gyaran jiki ba, ga mazan yanzu da dambanzan jaraba da fitina, duk kansu a waye yake sun riga da sunsan komai. Sosai Tayi niyyar zage damtse don gyara Nawaz ciki da bai, kuma bazata bari kowa ya san tana gurintaba har sai sanda ta gamsu ta tsuma ta da kyau da gyara yadda duk jarabar shi saidai yayi ya gama. °°°°° Ta chan gidan kuwa, koda Aseey ta fito Daga wanka bataga Nawaz ba sai bata damu ba don a tunaninta ta fita falour ne. Shiryawa tayi ta fita ta kira su Mummy Don aci abinci, kowa Yana dinning amma banda Nawaz, Mummy ce tace "kije ki kira Nawaz mana! Nifa Kunyar nan ta isheni haka, ace Mutum yayita ƙunshe kanshi a ɗaki bazai fito yasha Iska ba, kuma akan laifin daba nashiba. Amma idan taƙi ki rabu da ita kada ki matsa mata. Duk inda Aseey ke tunanin Nawaz ta shiga saida ta duba amma ba Nawaz ba alamunta, cike da fargaba ta karaso dining area ɗin tana cewa "innalillahi wa'inna ilaihiraji'un wallahi babu inda ban Duba ba amma Babu Nawaz Babu alamunta.. Miƙewa sukayi a tare, kamarya? Ina ta shiga to? Aikuwa duka suka bazama lungu da saƙo na gidan amma zance ɗaya ne, babu ita. Sosai suka shiga tashin hankali sunata salati da sallallami, Mummyn SARFRAZ ce tace "to ko guduwa tayi?" Da sauri Aseey ta shiga dakinsu tana dube dube, sai daga Baya ta fito idonta Duk yayi ja, "Wallahi guduwa tayi! Kuma bata ɗauki komaiba sai wayarta, harta kuɗin da Aayaan ya bata ɗazu da suka yi sallama bata daukaba... Tare su Mummy suka dada rafka salati haɗe da cewa "ita kuwa ina zata haka, Aseey kodai kinyi Mata Wani Abin ne? 😳😳 zaro ido Aseey tayi "Shikenan kuma!!! Wallahi Ni nasan dama wannan Abin a kaina zai ƙare, ku kanku da muke cikin gidan tare zargina kukeyi balle shi uban gayyar, Allah dai ya fidda Ni. Mummy ce ta kuma cewa "to koshi ya ɓata mata rai kafin su rabu? Duk ran Aseey a jagule tace "Ni ban saniba, sannan don Allah taya zakuce ko Wani abu nayi mata? Yanzu Aayaan yanajin wannan Kalmar taku akanta zai tsaya, kuma Mummy kinsan dai Yadda Aayaan yake da tijara idan aka taɓa abinda yakeso... "Af wato ke Yanzu fushi ma kikayi!? har kinada Lokacin yin fushi ga ƴar Mutane tayi ɓatan dabo. Mayafi kowa ya ɗauka suka fita cikin layin ko Allah zaisa su ganta ƙilan wani abu ta fita ta siyo, sosai suka zagaya duka layin amma babu alamunta. Basu suka dawo gida ba sai wajen Biyar saura, a hakan ma don sun gama cire raine, koda suka koma gidan Babu Wanda yabi takan abinci domin yunwar ma nemanta sukayi suka rasa. Iya fargabaar tafiyar Nawaz ce ke musu yawo a kwakwalwar su. °°°°° 🤣Shi kam Alh Aayaan ana chan ana fama, bai san wainar da Nawaz ta soya taba Aseey ajiyaba😂😂 sai Wajen ƙarfe Shida aka gama taron, Sannan ne yayi hamdala don yasan Yanzu zai samu Lokacin kanshi... Gurin Colonel yaje sukayi Sallama akan idan an kwana biyu colonel ɗin zaije chan Maiduguri gurinshi, dayake Aayaan ya amshi hutun wata uku da yake amsa duk Shekara. Mota ya ƙarasa ya shiga Inda securities ɗinshi suka dau hanya, "Daniel idan kaga wani store me kyau kafin mu karasa gida notify me pls" " Yes Sir" cewar Daniel Yana daɗa zuba idanuwan shi bisa titi. A daidai *M.R.G Plaza* sukayi parking, Sannan Aayaan ya shiga ciki, gurin ɗan kunne da sarƙa da zobuna ya ƙarasa inda yayi selecting ɗin wasu special na Gold Wanda ya siyesune a Matsayin kyautar da zaiba Nawaz idan yaje gida, tunda yasan ya ɓata mata rai kafin ya fita.... Biyan kuɗin yayi sannan ya koma mota suka dauki hanya, sai kuma suka kuma tsayawa a *A.M CAFE* Inda ya tsaya ya siyar ma MUHSIEN chocolate da ice cream, Basu kuma tsayawa a ko ina ba sai a Kofar gidan su sarfraz Wanda a Yanzu suka yada zango. Cikin gidan kuwa kowa zaune yake yayi jugum kamar yan zaman makoki, domin Mummy tayi yunkurin kiran baffa ta faɗa mishi Amma Mummyn SARFRAZ ta hanata tace Gara a Bari Aayaan ya dawo tukuna. Ita kam ta ɓangaren Aseey ba'a cewa komai, tasan Aayaan da ɗaukar zafi kuma ba Lallai ya fahimceta ba, zaune take Kawai Amma zuciyarta sam babu daɗi. Saida gudun bugun zuciyar kowa ya ƙaru jin sallamar Aayaan ta karaɗe cikin babban falourn *"ASSALAMU ALAIKUM"* Fuskarshi a sake alamun yana cikin farinciki, a sanyaye kowa ya amsa mishi jiki Babu kwari. Shikam Aayaan duk bai lura da halin da suke cikiba yace "sannunku da gida mummies da kuma Aunty Aseey! Murmushi sosai yakeyi inda ya karasa gaban Aseey yana ja Mata kumatu "sis yau kuma Babu welcome hug Koh" Ajiye shopping bag ɗin hannunshi yayi Tare Da cewa "Ga tsarabar passing out na kawo muku, but Bama Wani Abu bane special I think memo ne dasu snacks haka, may be kuma akwai T-shirt aciki.... Yanda yaga Babu wanda ya bashi attention ne yasa ya ɗago da kanshi yana karantar mood ɗinsu "mum meya faru? Ya naganku haka? Kowa shiru yayi don bayaso aji mutuwar Sarki a bakinshi. I am asking Amma Babu Wanda Ya kulani, wai me ya faru ne? Muhsien ne wanda dawowarsa daga bathroom kenan yayi fitsari yace "la Uncle ka dawo? Waigawa Aayaan yayi yana kallonshi "Na dawo muhsien" Aayaan yace yana maida kallonshi kan Aseey "to ke ki faɗa min tunda su sunki cewa komai. Kwakwalwar Aayaan Saida ta tsaya na ɗan wucin gadi, dalilin Muryar muhsin daya jiyo tace "Uncle Aunty Nawaz ta ɓace, har nemanta mukaje amma bamu ganta ba. Kafin Wani ɗan lokaci har goshin Aayaan yayi ruɗu-rudu da jijiyoyi _*"shin dagaske baku ga Nawaz ba??????*_ Ya faɗa da ƙarfi har Saida dakin ya amsa. Namma Babu Wanda Ya Iya bashi amsa sai muhsin daya Kuma cewa "Allah Uncle batanan, babu ita a gidan nan, kuma har waje munje dukanmu Amma bamu ganta ba ta ɓace" Be kuma Kula kowa ba ya juya da hanzari Zai fita, sai Sannan Mummy tace "Aayaan dawo! Kada ka fita!. Chak Aayaan ya tsaya a inda yake amma be waigo ba. "Aayaann ka dawo nace!, Dawowa Aayaan yayi ya tsaya a tsakiyar faloun dai dai saitin mummy, "mummy gani" sannan yayi shiru yana kallonta "Aayaann inaso ka nutsu ka maida hankalinka waje ɗaya yadda Zaka fahimci me zan faɗa maka, Yanzu idan ka fita ma ina zakaje? samu Guri ka zauna. Hakanan ya zauna a kan kujera badon zuciyarshi naso ba, sai don kasancewar shi mai tsananin biyayya ga mummy. Duka Abinda Mummy ta sani Game da ɓatan Nawaz nan ta zayyane mishi komai, ai kawai Sai Aayaan Ya juya ga Aseey. "Ina matata take? Kada kice zaku haɗa baki Kumin Irin wannan wasan, wallahi i can't endure it! Ni kaina Yanzu na Sani kuma na saduda cewa Nawaz itace raunina!. Tsalle Aseey tayi ta dire "haba Aayaan kaima kasan bazan taɓa haɗa baƙi da Wani don muyi maka Abinda zai Cutar dakai ba, Wallahi bro bansan inda Nawaz takeba. Miƙewa Aayaan yayi "Allah ki fito min da matata, ninasan dole akwai abinda ya faru, ko kinyi mata wani abu ne?, Nawaz bazata gudu hakanan ba. Aayaann abinnan fa ya fara isata, naga Babu yanda banyi akan ku zama intimate ba amma kaƙi yarda wai kai kana sonta kuma kanaso Saida yardarta tukuna.. Aigashinan, Wallahi nasan da ace ka kwanta da ita Babu yadda za'a yi ta gudu! Amma yanzufa? Tanada right a hannunta koda Auren tace batayi kaga dole a rabashi, amma da ka kwanta da ita Babu yadda zatayi dole ta zauna kodon kada ta zama ƙaramar bazawara. Shiru Aayaan yayi Kawai ya tsaya yana kallon Aseey domin yama kasa cewa komai, Mummy Dake gefe kuma cewa tayi "kinci uwaki aseey, muna gurin nan amma kike wannan fitsarar? Laillai wuyanki ya Isa yanka. Shiru Aseey tayi domin sai yanzu ma ta lura da ɓaramɓaramar data tafka. Saida Aayaan ya sauke wata gwauruwar ajiyar zuciya Sannan yace"to wallahi Aunty Aseey wannan Maganar ma da kika yi ta daɗa tabbatar min da cewa kinsan inda Nawaz take. _"Wai mu zama intimate!_ _wai in kwanta da ita! to ance miki Ni namijine?_ _*Toni macene!!!*_ *_i am impotent!!!!_* Kuma dama Ni ban auri Nawaz don ina sha'awar taba, sai don ina ƙaunarta.... Mum kam Kusan suma tayi a tsaye " meyasa Aayaan zaice shiba namiji bane shi mace ne? It means fa gabanshi baya aiki kenan😳 kada fa ace da gaske yake shiyasa all this while yaƙi yarda yayi aure.... Tawowa gurinshi tayi "haba my son! Pls kacemin kaiba impotent bane Please!. Juyawa kawai Aayaan yayi ya shiga ɗaki batare daya kula kowaba ya Maida kofar ya rufe. Ni dai matar Rasheed cewa nayi "wanga wace iriyar masifa ce?😳😳 Aayaann ɗinne mace kuma? To duk wanga rusheshen jiki nashi ya tashi ga banza kenan🤣🤣. Mummy kan faɗi take "lahaula wala quwwata illah billah, ya Allah kasa ba Gaskiya bane, nikam idan hakane ya zanyi da raina?..... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ta ɓangaren SARFRAZ kuma Ganin wasu Masu kiwon raƙuma yayi sunzo wucewa ya bisu yanata kallon raƙuman domin sun bashi sha'awa. Chan dai Hassu ta fito Daga bukkar da suke dafa abinci taga bata ganshi ba, ɗaki ta duba namma babu shi. Sai kawai ta nufi tirken shanu don Yawancin lokuta Anan take samun shi. Abin ya ɓata mamaki Ganin babu shi Anan, miƙar hanya tayi tana kwala mishi kira "SARFRAZ! SARFRAZ!! SARFRAZ!!! Amma ina aiko keyarshi babu. Ganin da gaske babu shi yasa Hassu ta rushe da ihu tana Bin Hanyar gidan malam tana zunduma ihu...... Namma dai Ni matar Rasheed cewa nayi 😳😳😳 chakwakiya. °°° Nawaz kam Saida yamma tayi taji duk kewa ta kamata, ji takeyi ma meyasa ta gudo tunda dai Basu Aseey bane sukayi mata laifi Aayaan ne, take taji bata kyauta ba ko ya Mummy da Aseey zasuyi idan suka buɗe Ido basu gantaba? Shi kanshi Aayaan ɗin Saida taji kewarshi, hakanan ta kasa sakin jikinta, domma Inna tanata janta da hira.... Himma bata ga rago! Domin inna harta hada Wasu saiwoyi da sassake dasu kayan kamshi da mazarkwaila ta dafa ta juye a bokiti, jira takeyi ya huce taba Nawaz tace ta maidashi Ruwan Shanta.... Ƙaƙa-ƙara-ƙaƙa! Nifa har na ƙosa naji yadda za'a yi a shafin gaba, domin akwai tirƙa-tirƙa da yawa. Gashi nan dai Inna harta fara tsuma Nawaz 😂 gashi kuma Aayaan Yace shi macene😳, Toya abin zai kasance???? Shi kuma SARFRAZ yabi raƙuma! Ga hassu na zunduma ihu 😳😳😳😳 Koya Aseey zasu ƙare da Aayaan kuma🤣🤣🤣 shidai ya dage akan saita fito mishi da matarshi... 🧐🧐Anya Mummy zata iya Bacci ma kuwa? Gata mayyar ƴaƴa gashi kuma Aayaan yace babu kayan aiki🤣🤣🤣🤣🤣🤣 Don haka saiku zage kuyi comments da sharhi yadda zanji daɗin kawo shafin gaba, Idan ba haka ba kuma kuji wayam, har sai zuwa sanda naga zan iya turo muku.. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 47* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Koda Aayaan ya shiga ɗaki kasa zama yayi, yama rasa me zaiyi yaji daɗi! Idonshi gaba ɗaya ya kaɗa ya koma jaa, jikinshi kuma har wani irin huci yake fitarwa. Bathroom ya shiga ba Tare Da ya cire ko ɗaya daga cikin Kayan jikinshiba ya sakarwa kanshi shower 🚿, yafi ƙarfin minti Talatin a tsaye Ruwan yana zuba a jikinshi Sannan ya samu ya cire kayan yayi normal wanka, babu Abinda ya ragun mishi daga raɗaɗin dayake ji a cikin zuciyarshi illah zazzaɓi da yaji ya rufe shi likaci guda. Bathrobe yasa Sannan ya fita daga bayin zuciyar shi na tunani kala kala, yama kasa ko shirya wa, ko mai bai iya shafawa ba, komawa kan gado kawai yayi yaja duvet ya rufe jikinshi Sakamakon wani Irin sanyi dayaji yanaji, Sannan ya dau wayarshi wadda ke ajiye a gefe, Number Nawaz ya nema ya kira, Amma sai akace switch off. Sosai yake mamakin wai me akayi wa Nawaz da har ta yanke wannan tsatstsauran hukuncin? Shi Yanzu ko nemanta zaiyi baisan ta inda zai Fara ba. Shiyasa yaso sanda Mummy ta faɗa mishi cewa Nawaz matar shice da an sanar da Nawaz ɗin itama. Gallery ya koma inda ya nuno photon Nawaz ya ƙura mishi ido, "why did you choose to run away? Why did you not think of what will happen before going, how i wish you were here when I'm back..... Haka dai Aayaan yaketa magana shi kaɗai sai kace Nawaz ɗin tana zaune a gaban shi.. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sosai Hassu ke ihu tana tafe kuma tana kwalawa SARFRAZ kira ga duhun dare ya fara sauka, saura kaɗan ta ƙarasa gidan baffa ta hango wani Cikin raƙuma kamar SARFRAZ, ai kuwa da gudu ta kwasa zuwa gurin tana kwalawa SARFRAZ kira.... Waigowa SARFRAZ yayi yana dariya "Hassu zo kigansu Masu kyau, mu bamuda irin wadannan sai dai irin su gwalbo... Wani tuƙuƙin baƙin ciki ne ya turniƙe hassu "Wato yanzu da Ban fito ba da Shikenan binsu zakayi, Ni na taɓa ce maka idan kaga Wasu ka bisu koda mutane balle raƙumi! Saroro SARFRAZ ya tsaya, exactly dai Kamar yadda yara sukeyi idan sunyi laifi, harara ta balla mishi "ba tsayawa zakayi ka zuba min ido ba, daka ɓace daka gane kuranka.... Juyawa tayi ta tafi ba tare data ce zo muje ba, ai kuwa shima saiya bita da gudu yana cewa "kijirani mu tafi" Hassu da baƙin ciki ya dameta akan Cewa da Yanzu sarfraz ya ɓace data shiga uku duk saitaji haushin shima takeji, ƙin kulashi tayi taci gaba da tafiyarta. Aikuwa SARFRAZ Yana ƙarasawa kusa da ita ya faɗa jikinta yana cewa "inata cewa kijirani anma kikayi banza dani! Taga-taga Hassu tayi zata faɗi sai kuwa ya taro ta suka faɗi ƙasa tare yana dariya, Cikin kwayar idonta yake kallo itama Haka, Sanin cewa a Banza "wai an yakushi kakkausa" tasan shi bema san meyakeyiba, ta tashi tana kakkaɓe zaninta. Daɗa riƙo ta yayi ta faɗo jikinshi yana ƙara cewa "meyasa baki jirani ba?" "Don Allah SARFRAZ ka kyaleni mana" hassu tace tana tureshi daga jikinta, "kaso ka kasheni wallahi, fisbilillah da Allah besa na fito yanzu ba Shikenan ka ɓata kenan? "Ni dai Gaskiya har dai kanason in cigaba da zama ƙawarka kada ka kuma bin koma me kagani" "To bazan kumaba"; SARFRAZ yace yana riƙe hannun Hassu tare da haɗa su guri ɗaya da nashi yana sarƙafe yatsunshi cikin na Hassu, sannan suka dauki hanyar komawa gida. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Jama'a wai kam Babu Wanda ya taɓa cigiyar umma, anya kuwa? Kodayake dama ai mutum mai baƙin hali bashida farin jini, amma dai yau Ni zan leƙa ko don naga ƙwaƙwaf! Sauri sosai umma da fauziyya sukeyi a cikin dajin, wanda gaba da bayan shi babu alamun gida sai dai bishiyoyi da ciyayi kala-kala kuma ga magriba ta sanyo kai don garin har ya fara duhu. "Fauziyya wai har Yanzu bamu iso bane? Nifa na fara gajiya! Cewar umma wadda gaba ɗaya ta tattare zaninta gefe guda saboda Uwar tafiyar da suka sha. "Umma kiyi hakuri mun kusa saura kaɗan, muna wuce waccan bishiyar kanyar Zaki hango bukkarshi, fauziyya tace tana nuna saitin bishiyar da yatsanta. " To Shikenan! Wallahi tafiyar ce ta isheni, tundazu fa muke tafiya amma munki kaiwa sai kace waɗan da zasuje ƙarshen duniya.. Kallon Umma fauziyya tayi sannan tace "to umma naga ai biyan buƙata yafi dogon buri! "Nima ai don burina ya cika ne shiyasa na yarda nayi wannan Uwar tafiyar amma wallahi da Babu abinda ya isa yasa nayi ta. Saida suka daɗa tafiyar kimamin minti goma tukuna suka isa bukkar, ita kaɗai ce a cikin dajin, babu gida gaba babu a baya, amma dayake zuciyarsu ta bushe babu ko alamun tsoro suka duka suka shige cukin bukkar, zaune yake baƙikƙirin dashi Hakazalika idanunsa ma jajaye ne gwanin ban tsoro. Gefe suka samu suka zauna tare da cewa "ran boka ya daɗe" "Hahahahahahahaha haha "ya saki wata Uwar dariya Kamar kukan jaki "kada kuce zakuyi bayani! Na rigada nasan Abinda ke tafe daku. kinasone ayiwa ƴar kishiyar ki asirin baƙin jini Yadda Babu wanda zai taɓa aurenta, sannan Abu na biyu shine, kinaso Yadda suka tafi suka barmiki gida ke kaɗai, to a rufe bakinsu kada su dawo Sannan a shashantar dasu game da gidan... Zaro ido umma tayi "ya akayi ka sani? Daɗa kyalkyalewa da dariya yayi Sannan yace "au an faɗa miki Ni na wasa ne? To bari kiji idan ma kinzo da wasa to Gara ki shirya kisan ba gurin wasa kika zoba. Yanzu abinda za'ayi shine zaki kawo ƙasar da aka gina fadar Sarkin sin tun karni na takwas, sai kuma ruwan tekun ƙarshen duniya, da kuma gashin girar gawar fir'auna dake ajiye a gidan tarihi a ƙasar masar, muddin waɗan nan abubuwan suka haɗu to zakisha mamaki domin sai dai yarinyar ta mutu a haka, don babu wanda Zai taɓa jin sonta koda dai dai da girman kwayar zarra ne a zuciyarshi, kuma su da dawowa gidan nan har abada, ke ingaya miki ko kashe su kikeso ayi tsaff zan aika su lahira ba Tare Da Wani shamaki ba, mufa nan babu wasa a harkar mu sam. Sosai farinciki ya kama umma jin bayanan da boka ya gama faɗa, amma damuwarta ɗaya a ina za'a samo Kayan daya lissafa, cewa tayi "boka Kada a kashe su, nafison su rayu Amma cikin ƙasƙanci da tozarci Yadda da kansu sai sunyi dasunsanin zuwansu duniya... To kuma matsalar duka abubuwan daka lissafa banida haryar dazan iya samosu! Wani yare boka yayi tare da zazzare idanuwanshi masu kama da bushasshiyar gauta (ɗata) Sannan yace "a cikin rafanai an samu Wanda yace zaije yanzu ya dawo cikin minti biyar ya Kawo komai amma da sharadin za'a yanka mishi baƙin raƙumi... Zaro Ido umma tayi, ga ƙoshi ga kwanan yunwa! "To Ni yanzu ina zan sami baƙin raƙumi? "Kada ki damu, Akwai aljanin da zansa Wanda zaiyi shigar Mutane yaje chan Niger ya siyo, Yanzu kuɗin Kawai zaki bada.. Ɗan murmushin samun nasara Umma tayi "to boka nawane kuɗin? Washe baki boka yayi Sannan yace ba wani yawa ne dasuba, dubu ɗari shida ma ya isa! Kuma ina Daɗa tabbatar Miki da cewa har dai akayi aikin nan to su da samun farin ciki kar harshen rayuwarsu.... Shiru Umma tayi Sannan tace "gaskiya kuɗin hannuna dubu ɗari da saba'in ne kuma Gashi inason aikin cikin gaggawa! Washe baki boka yayi tare da cewa "kawo ɗari da saba'in ɗin, inyaso gobe saiku dawo kafin nan ma na gama haɗa maganin Kawai saiku tafi dashi idan kunzo.... Sosai Umma taji daɗi harda yi mishi godia Sannan suka tashi suka fita daga bukkar, ita dama fauziyya Yar kallo ce, Babu abinda ta furta illa dai sai taji Abin Kamar yayi yawa, Domin Nawaz bafa Ita ta zaɓar wa kanta Uba ba, kuma ai ummi ce kishiyar umma ba Nawaz ba, yaza ayi a hanata yin aure. Ƙunɗinbala tayi tace "umma sai naga abin kamar yayi yawa! Naga Babu ruwan Nawaz, ba Gara koma meye ayiwa ummi ba Tunda ai Ita ta Aure Miki miji ... Kama haɓa umma tayi "Lallai fauziyya! Yaushe kika koma Malama? Ni kike wa wa'azi? To lallai raini ya Fara shiga tsakaninmu, nanfa umma ta fara faɗa, inda take shiga batanan take fitaba... Hakanan fauziyya Tayi gum da bakinta bata kuma cewa komaiba... Ni kam matar Rasheed nace " mara rabo dai yashiga uku, boka ya zurma umma kuma ya amshe Mata kuɗin ta da imaninta. Kuma dai Nawaz naga amarya take a Yanzu, don haka umma kin makaro🤪🤪 °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sosai inna tayiwa Nawaz wayau domin dama tasan Nawaz ɗin bawai ta cika shiga Cikin kawaye da yawa bane, balle ace tasan magungunan mata ba. Bokitin maganin ta ajiye a gaban Nawaz "yata ga magani na Kawo Miki, inaso ki Maida hankali Wajen shanshi domin maganin sammu ne, kuma Tunda kikacemin umma ta Turo ayi miki fyaɗe naji zuciyata ya kasa Zama guri ɗaya, Domin Duk Wanda Zai iya sawa ayi maka fyaɗe to Babu abinda bazai Iya yi maka ba, don haka ki dage sosai da shansa. Har mazarkwaila ma nasa Miki aciki saboda kiji daɗin sha, kuma akwai na gari shi da nono akeshanshi, saboda shi na kambun baka ne da maita, gobe idan Allah ya kaimu zanje kasuwa sai insiyo mana nono galan ɗaya, Sai Musa a fridge duk sanda zamusha sai mu ɗiba. Wani sabulu a cikin ƙaramin bokiti ta mikawa Nawaz ɗin "Kinga wannan shima na sammu ne, domin a cikin hadin harda ganyen magarya da ƙaiƙayi koma kan mashekiya aka zuba, zaiyi Miki magani kuma zai gyara Miki fata sosai. Insha'Allah hardai kina gidan nan saikin gaji da magunguna, domin so nakeyi kome umma zatayi yazama tayi a banza, kuma Sannan inaso ki dage dayin azkhar sosai, kinji daughter? Godiya sosai Nawaz tayi mata, Tare Da ƙara jin ƙaunarta a Cikin zuciyarta, tasan cewa babu wanda zai iya yi mata haka idan aka cire ummin ta. Sam magungunan basu damu Nawaz ba, shan abinta take tayi domin dama ita bame gudun magani bace, don iya ranar ta kusa shanye wanda inna ta dafa, barin akwai zaƙi🤩... Nidai cewa nayi "zaki yabawa Aya zaƙin ta" Ita kuma ta ɓangaren inna daɗi taketaji kasancewar bata sha wahala ba, kuma inda abinma yazo mata da sauƙi bata daɗe Da dawowa daga Niger ba, duk ta tawo da magunguna kala kala, Ashe zasuyi mata amfani.... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sosai zazzaɓi ya rufe Aayaan domin harta duvet ɗin daya rufa dashi Saida yayi zafi, gakuma wani uban sanyi da yakeji. Mummy ce tsaye a bakin kofa tanata bugawa "Aayaan! Aayaan! Aayaann!!! Please kazo ka buɗe min kofa, please my son! Aayaann Yana kwance ya jiyo Muryar mummy, hakanan don Babu yadda ya Iya yasa ya miƙe jikinshi yana rawar sanyi yaje ya buɗe ƙofar Sosai tsoro Ya kama mummy, Domin bata taɓa zaton abun har yakai hakaba! Kamashi tayi nanma taji jikinshi rau Kamar garwashin wuta. "Aayaann Yanzu fisbilillah Abinda kayi ka kyauta kenan? Kasan bakada lafiya shine ka Shigo ka rufe kanka a ɗaki? Ko abinci fa baka ciba, Yanzu don Allah ki yadda jikinka yayi zafi, ya kakeso nayi? Da ɓacewar Nawaz zanji ko da ciwonka? Fashewa Aayaan yayi da kuka "Mummy don Allah kicewa Aunty Aseey ta fitomin da matata, idanma tayi hakane don ta gane ko inasonta da gaske, to ace Mata wallahi ina sonta kuma ina ƙaunarta. Sosai tausayin Aayaan ya kama Mummy, lallai wanga Abu babbane, ta manta rabon da taga hawaye a idon Aayaan amma yau gasu nan suna kwarara, Sam bataga lefin shiba don dama Mutane da yawa sukance duk Wanda Bai taɓa yin soyayya ba to Idan ta kamashi Abin Baya yin kyau..... Patting bayanshi takeyi a hankali"I'm sorry Aayaan, Insha'Allah i Will do My very Best don ganin matarka ta dawo, kuma Aseey ma zan tsawwala mata yadda Idan tasan inda Nawaz ɗin take Dole ta faɗa min.. Hakuri Mummy taketa bashi, shikuma ya dunkule Guri ɗaya a jikin mummy Kamar zai koma ciki. Çikin hila da dabara irin ta iyaye mummy tace "Aayaan nifa haihuwar farko inasone Nawaz ta haifi Mace saboda insa mata sunan twins ɗina, hope zaka bani? Mummy Kawai kiyi iya kokarinki na Ganin Nawaz ta dawo domin jikoki ma saikin gaji dasu, harda ƴan bibbiyu zata riƙa haifar Miki, ammafa idan ba Nawaz bace ta dawo bani Babu yin Aure don haka ki taimaka ta dawo ko don ki samu jikokinki... "Daɗi Kamar ya kashe Mummy, dama dabara tamishi don taji cewar wai shi ɗin macen ne ko kuwa Kawai ya faɗa ne? Yanzu ta gane Cewa bacin raine yasa yacewa Aseey haka, Mummy kenan! Hankali dai ya kwanta tunda anji Aayaan lumui yake...... Aseey kam itama haɗa kayan ta tayi akan gobe idan su Mummy suka shirya zasu koma Maiduguri ita kuma ta tsaya a Kano ta hau jirgi ta koma gida, don taga alamun wannan zuwan kamar Babu Sa'a... Ina jiran sharhi *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 48* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Sosai Mummy ta kwantar wa da Aayaan hankali, inda tace mishi kada suyi garajen faɗawa baffa cewa Nawaz batanan har sai sun koma Maiduguri, Saboda su Fara zuwa gidan su duba da kansu, idan kuma akaci Sa'a chan taje Shikenan... "Aayaann promise me you will not cry again" Mummy tace tana goge mishi Fuskarshi da tafin hannunta. Gyaɗa Kai Aayaan yayi tare da cewa "mummy bansan ma sanda nayi kukanba, kawai nima zubar hawayen naji. "Kada ka damu my son, Nawaz ta chanchanci fiye da kuka, domin duk inda macen arziki take takai, yarinyar akwaita da kiyayewa gason kyautata wa na kusa da ita, Abinda yafi birgeni shine kunyarta da Addininta, inasonta dakai sai dai banso abin yazo a haka ba, naso ace da kanku kukaga juna kukace kunaso. "To Amma ko hakan ma babu matsala tunda kai kana sonta, kuma Nasan zaka kula da ita sosai, Ni burina dama kada a shiga haƙƙinta. Ajiyar zuciya Aayaan yayi Sannan yace "Nifa tun randa na fara ganinta ta birgeni, amma bansan sanda sonta har yayi min irin wannan kamunba! But i know special habits ɗin ta suna bani sha'awa.. Dafa kanshi Mummy tayi "Stop worrying yourself Insha'Allah she Will be back! And kuma bi'iznillah Zaku haɗa kanku yadda har sai wasu sunyi burin dama sune ku. Saida ta tabbatar ta ragewa zuciyar Aayaan raɗaɗin da takeyi tukuna sukayi Sallama ta koma ɗaki. Fitarta keda wuya Aayaan ya tashi ya zauna, jingina yayi da fuskar gadon yana cire security ɗin wayarshi. Number Nawaz ya kira, still dai switch off. Shiru yayi yana tunanin ta ina zai fara ne? Ai kuwa dabara ce ta faɗo mishi ta yadda Idan yaci Sa'a Nawaz zata iya dawowa da kanta.. Message ya rubuta Kamar haka 👇 _*ASSALAMU ALAIKUM*_ _*Ina Fatan Duk inda kike ki kasance cikin aminci da kariyar Ubangiji, da fatan kuma kina lafia, ya gajiyar guduwa babu sallama?*_ _*Bansan Wane irin Babban laifi na aikata miki ba wanda har ya shafi kowa, haƙiƙa hankalina ya tashi sanda na dawo akace an nemeki sama ko ƙasa babu ke kuma ba'a San Inda kike ba.*_ *_mummy tana Cikin matsanancin tashin hankali, ita da Aunty Aseey da ɗaya Mummyn babu Wanda yaci Wani abu. Kowa yana Cikin tashin hankalin ba'a San Inda kikeba_* *_Don Allah ba don halina ba idan saƙon Nan ya isa gareki ki taimaka ki dawo, Kuma nayi miki alkawarin bazan Kuma Yi miki abinda Bakya soba, Idan ma Bakya son ganina zan Iya barin gidan, and kuma Insha'Allah gobe zamu koma Maiduguri.._* *_Naki mai ƙaunar ki har cikin ruhi, C.A MUHAMMAD MAI GORO_* Sannan ya tura mata Tare Da saita delivery report yadda idan saƙon ya shiga zai sanar dashi, ta haka ne zai gane idan ta kunna wayar... Tashi yai ya shiga bathroom ya ɗauro Alwala, Sannan ya shimfiɗa praying mat ya tada kabbara donyin sallar nafila ya roƙi Allah akan ya Bayyana mishi Nawaz.. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Nawaz kam kwance take Amma abin Duniya Ya isheta, saboda duk juyin da zatayi Sai Aayaan ko Aseey ko mummy wani ya faɗo Mata a zuciya. Harta MUHSIEN saida taji kewarshi, barinma mummyn sarfraz da take ganin kila ta ƙara ganin baƙinta Tunda dalilinta SARFRAZ ya ɓace gashi kuma Yanzu ta gudu. Wayarta ta janyo donta kunna ko ɗan dannawa tayi kila ta rage dare, domin sam babu barci a cikin idonta.... Chan kuma wata zuciyar tace "Kada ki kunna Nawaz! Ƙilan yanzu ana chan ana trying ɗin Number, kinga Idan tsautsayi yasa kika kunna kin jawa kanki. Maida wayar tayi ta ajiye sannan tamike ta shiga bathroom ta ɗauro Alwala.. 🤩🤩Ruhi ɗaya kenan, Aayaan Yana qiyamul layli saiga Nawaz itama ta tada iƙama.. Kusan haka asuba tazo ta riske su a tsaye, domin dogayen surori duk suka karanta... Nawaz kam sai bayan tayi sallar asuba taji wani bala'in barci ya kamata, ai kuwa babu shiri ta koma ta kwanta, Domin ji tayi Idan batayi barcin ba komaima zai iya faruwa, don jinta rake kamar Wadda tasha kwaya. Shikam Aayaan wanka yayi Sannan ya fita ya faɗawa securities ɗinshi cewa su shirya don Yanzu zasu ɗauki hanya. 😭😭😭😭😭😭😭😭 Mummy da Mummyn SARFRAZ ne keta faman kuka, duk ankai duka kayansu mota amma su sun rungume juna sun kasa rabuwa sai kuka sukeyi, itama Aseey dake tsaye a gefe sai taji idonta ya cika da kwalla. Aayaann ne yace "please kuyi hakuri, Insha'Allah bawai an rabu bane, har abada ana tare Insha'Allah, kuma nayi muku alkawarin Cewa duk Wanda yakeso yaga ɗaya daga cikin ku, Kawai ya kirani a waya zanzo na kaishi, idan ma bana Free to zansa securities ɗina su kaishi. Sosai idonsu ya kumbura kuma yayi ja, sakinta mummyn Aayaan tayi ta juya ta fita daga faloun ba tare data ko waigoba, Aayaan dake tsaye ya Kalli mummyn sarfraz yace "mum i promise zan riƙa zuwa lokaci bayan lokaci, kuma zan riƙa kawo miki mummy, and I will do my best akan binciken inda zanga SARFRAZ... Haɗa hannunta tayi guri ɗaya tare da cewa "Nagode Aayaan, Allah ya kaiku lafiya... Shima Aayaan saiya juya ya fita, be shiga motar su Mummy ba saboda beso damuwa tayi mishi yawa, sai kawai ya shiga ɗayar motar ya kwanta a back seat tare da rufe idonshi, ranar da zasuzo Zaria ya tuna yadda sukaita drama da Nawaz, amma Yanzu babu ita.... Tunani yakeyi yanzu Abin ya zama biyu kenan, ga SARFRAZ ga Nawaz! Ta ina Zai fara ma Oho. Mummy ma zaune suke ita da Aseey Kowa yayi jugum Duk zuciyarsu babu daɗi, Aseey tana tunanin anya kuma tafiyarta zata yiwu? Duba da halin da mumy take ciki ga kuma Aayaan shima, muddin ta tafi yanzu tasan cewa zasuyi bata damu dasuba, ko Babu Komai ya kamata ta Zauna na ɗan Wani lokaci har zuwa sanda za'a samu sauƙin abin. Ita kuwa mummy tunanin take yadda mummyn sarfraz ta ɗauke ta Kamar yayar ta, sam bata ɓoye mata komaiba, sannan ta nuna mata zallar ƙauna, anya ma akwai abinda zatayi Mata dazai fanshi ƙaunar data nuna mata? Sai misalin biyar na yamma suka isa gida, Kowa jikinshi babu kwari, don haka babu wani zumuɗi sai ma tarin damuwa a tare da kowa. Mummy na buɗe ƙofar ta shige falour, inda Aseey kuma ta tsaya ta kasa shiga sai muhsien daya kwace hannunshi yabi bayan mummy. Koda Aayann ya fito daga ɗaya motar be lura da Aseey ba Saida yazo gaf da ita, murmushi yayi yace sister Yau Sam bamuyi magana ba! Hope dai kina lafiya? Ɗazu muhsien Yace min wai kince mishi kanki yana ciwo. Hope ya Dena? Shiru Aseey tayi tana kallon shi, mamakin halin Aayaan takeyi sosai, Yanzu zai yi faɗa Yanzu kuma zai chanza Kamar bashiba, "Aunty Aseey ko fushi kikeyi da ɗan kanin naki? Pls ayimin afuwa nasan ban nuna respect ba. Murmushi Aseey tayi "bro i can't be angry with you, kawai dai ina tuna sanda kake daka min tsawa ne akan saina fito maka da matarka." "Please Aunty Aseey kidena tunawa, wallahi Bansan meyahau kaina har hakan ta faruba, ban san meyasa abu hardai ya shafi Nawaz yake rikitani ba" "Soyayya ce tasa hakan!" Aseey tace tana ja mishi gefen kumatunshi, sannan ta kuma cewa "Ashe Soyayyar da kake yiwa Nawaz ta wuce tunanin me tunani, Gaskiya najiwa Nawaz daɗi, harna ƙosa ta dawo inga yadda za'a kaya, dukda dai kace kai ɗin mace ne! Toshe mata baki Aayaan yayi yana dariya "Aunty please kiyi shiru kada ki ɗauki zunubi" sannan ya saketa ya shige faloun da gudu yana dariya.... Murmushi Aseey tayi "inasonka Aayaan, bazan taɓa Iya yin fushi da kaiba, kana birgeni saboda kokayi fushi kana sauka da wuri, gashi idan kayi laifi babu girman kai zaka ba Mutum hakuri. Sanin Cewa tuni Aayaan yayi gaba bema san tana yiba yasa itama ta shige faloun tare da shigewa dakinta.... Wanka Aayaan yayi Sannan ya samu guri ya zauna tare da janyo laptop ɗinshi gabanshi, ɗan dube-dube yayi tare da rufe laptop ɗin yana tureta gefe, me kuma ya tuna Oho sai kuma ya janyo laptop ɗin da sauri yana jona wata waya a jiki. Tarwai Nawaz ta fito ta cikin Laptop din, zaune take a bakin gado riƙe da Alqur'ani tana karantawa, forwarding yayi sannan ya danna play, still Nawaz ɗin ce ta kuma fitowa amma yanzu ta fito daga bathroom ne ɗaure da towel, zama tayi akan Kujerar make-up tana janyo lotion, sosai Aayaann yayi shiru yana kallonta har ta gama ta tashi taje bakin wardrobe ta ciro kaya, babu shiri Aayaan ya kifa laptop ɗin ganin Nawaz ta zare towel ɗin dake jikinta.. Ruf da ciki yayi sannan ya janyo pillow ya rungume, a hankali ya furta "were r u now! Rufe idonshi yayi yana ganin laifin kanshi don gaba ɗaya mood ɗinshi ya chanza, amma ai laifinshi ne! Meye na ganin ƙwaƙwaf. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Nawaz kam ba ita ta tashi ba sai misalin ƙarfe sha ɗaya da rabi, ai Babu shiri ta diro daga gadon tana salati, koda ta fita falour shiru tayi tana bin ko ina da kallo domin inna ta gyara komai ga ibincima ta jera a center table alamun ma ta daɗe da gama wa. Sam bata ji daɗiba, taso Ace ita tayi komai. "Ƴata kin tashi?" Nawaz ta jiyo Muryar inna, ɗaga kai tayi cike da kunya sannan tace "barka da hantsi inna, don Allah kiyi hakuri inna wallahi Bansan ya akayi ban tashi da wuri ba. " Meye na damuwa? Na leƙa naga baki tashiba shine nace bari na barki ki huta... Gashi ko karyawa bakiyi ba. Murmushi Nawaz tayi ''inna kada ki damu dama bana karyawa da wuri, fita tsakar gida tayi nanma tsaff a gyare kuma an shareshi tsaff. Duk sai taji kunya ta kamata, yanzu duk ina Cikin gidan nan inna tayi aikin nan, gaskiya ban kyauta ba.. Ciki ta koma donyin wanka, a falour sukaci karo da inna "yauwa Nawaz dama Inasone inje kasuwa, mezan siyo Miki? Ɗan murmushi Nawaz tayi"babu komai inna, Nagode. "Ai dama nasan ba Lallai ki faɗa ba, kiyi sauri ki karya saikiyi wanka, idan kuma wankan zaki farayi to, Nidai na tafi saina dawo.... " To inna a dawo lafiya;" Nawaz tace tana ɗaga mata hannu. Misalin ƙarfe uku Inna ta dawo daga kasuwar riƙe da kaya niƙi niƙi, tayata kwasowa Nawaz tayi suka shiga ɗaki dashi, aikuwa Duk yawancin siyayyar ta Nawaz ce, don haɗin sabulun gyaran fara ne dasu Dilka, sai kuma Madara da zuma da dai sauransu..... Wasu ƙarin magungunan inna ta kawowa Nawaz tace ta cigaba da Amfani da su Kamar yadda takeyi da sauran, sai dai Yanzu harda wanda za'a sha da zuma da madara. Wannan karan kam saida Nawaz taga kamar magungunan sunyi yawa, amma sanin cewa inna bazata cutar da ita ba yasa ta kawar da zancen daga zuciyarta. Da yamma bata bari inna ta kuma yin komai ba, ita ta daɗa share gidan tayi wanke wanke ta ɗora wani sabon abincin wanda zasuci da dare... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Washegari..... Zaune Aayaan yake a stool yana taje kanshi alamun yanzu ya gama shiryawa, wayarshi ya ɗauko yana duba sakon daya Turawa Nawaz kota gani, aikuwa baiyi delivered ba "it means bata ganiba kenan" yace yana yana dafe kanshi. Dai dai nan kuma wayarshi tahau ƙara, koda ya Kalli screen ɗin saiyaga Farouk ke kiranshi, Aikuwa yaji daɗin kiran saboda dama kiranshi yakeso yayi yanzu, "yooo ya dai" "Alhamdulillah" Aayaann yace yana miƙewa... "Ganifa a compound, nakai minti goma Acikin gidan nan, "meyasa baka shigo ciki ba?" "Hakanan wajen ne naji yamini daɗi yau Wallahi. "Okay to bari na fito!" Sannan ya nufi kofa ya buɗe zuwa falour, a dining ya tarar da Aseey tanaba muhsien abinci ita kuma Mummy tana zaune riƙeda hisnul Muslim tana karantawa, tsaff take kamar ba ita bace jiya take cikin tashin hankakiba, "mum zan fita, Farouk yana waje yana jirana!" "Allah Sarki Farouk meyasa be Shigo ba, kace ina gaishe shi, saika dawo. " Bro a dawo lafiya" Aseey tace tana ɗaga mishi hannu. Murmushi yayi "Insha'Allah dear, muhsien babu magana? Sannan ya juya ya fita zuwa harabar gidan... Zaune ya tarar da Farouk a saman mota, ganin Aayaann ɗin ya fito yasa Farouk ɗin ya diro daga motar tare da nufar shi cikin sauri, rungumeta juna sukayi sannan sukayi musabaha. Sosai suka gaisa inda Farouk yayi mishi ban gajiya, cikin mota suka shiga suka zauna, Farouk a driver seat Aayaan kuma a gefen mai zaman banza.... Farouk ne yace dama nazo na ɗaukeka ne muje kauyen fulanin nan, kasan bayan munyi waya naje har gida na dubashi. "Gaskiya ka kyauta, Toya jikin nashi? "To da sauƙi zance dai, amma dai jiya iyau, don koda naje tarar wa nayi yanata ihu waishi sai ansiyo mishi ice cream, gashi namijin bayanan sai macen, infada maka haka na kwaso su muka fito gari na siyar mishi sannan na maida su.... Ai ranar naga rukici.... Murmushi Aayaan yayi "to muje but Farouk wallahi ina cikin wani hali! Amma it's a long story.... Shiru Farouk yayi Sannan yace "koda na ganka na lura Akwai Abinda ke damunka, but saina zata ƙila daga barci ka tashi, Amma hope it's not serious... Fita da motar Farouk yayi daga gidan suka dau hanyar, sannan ne Aayaan ya Fara bashi labari tun randa suka haɗu da Nawaz a daji har zuwa bikinsu da guduwarta. Farouk kam jin abin ya rikayi Kamar mafarki, "Aayaan Are You alright? Wai kana nufin wannan abun a gaske ya faru? Kodai Wani littafin ka karanta kake bani labari... " Farouk zaka soma Koh! Nifa dama shiyasa wani zubin banason Neman Shawara a gurinka saboda saika gama yiwa Mutum shakiyanci tukuna.... "Afwan! Kaina bisa wuya abokina" farouk yace yana gyara fuskar shi Irin da gaske ɗin Nan yake.. Dai dai Nan ya iso bakin bukkar su hassu, parking yayi suka shiga harabar gidan suna sallama, ai kuwa Muryar Aayaan ce ta maƙale a wuya, Domin wani yagani sak Kamar yanda yaga SARFRAZ a photo, tabbas wannan SARFRAZ ne Duk da ban ganshi a fili ba amma wallahi shine.... Da gudu ya ƙarasa kusa dashi Yana cewa "SARFRAZ, kaine? Bandi dake gefe yana fama da SARFRAZ akan yaje hassu tayi mishi wanka ne yace"kai waye??? "Ni yayan shine " Aayaan yace babu ko ɗar a zuciyarshi, Hassu Dake gefe riƙe da kwandon wanka tace "wallahi ko kai waye baka isa ka rabamu ba, Sannan ta kalli likitan tace " kai likita haka mukayi dakai? Bacewa kayi zaka memo mana taimako akaishi ayimishi maganiba, to meyasa ka nemo ƴan uwanshi??? Ɗago Kai Aayaan yayi Yana kallon hassu wadda tayi kicin kicin da rai Ina jiran sharhi, yaudai SARFRAZ ya dawo💃💃💃💃💃 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 49* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Sai wani mazurai takeyi, ita ala dole babu mai rabata da sarfraz. "Sarfraz zo nan!" cewar hassu tana daɗa cin magani, Ai kuwa da sauri sarfraz ya miƙe ya karasa kusa da hassu, shima sai kallon Aayaan ɗin yakeyi. Farouk ne yace "hassu ki barshi yazo gurin yayan shi mana, bakiga sunyi kama da juna ba? *_(Shi ɗin ma bawai yasan shi bane illah dai yagane SARFRAZ ɗin da Aayaan ya gama bashi labarine, duba da Yadda kamanninsu ya nuna a fili)_* Chuno baki Hassu tayi sannan tace "bazai zoba" Tare Da rungume sarfraz ɗin. Shima SARFRAZ saiya ƙara rungume hassu sannan shima yace "bazai zoba". Aayaann kam sai abin ya bashi dariya yadda SARFRAZ da Hassu suka rungume juna kamar zasu haɗe, ga mazuran da hassu takeyi, bandi ya kalla Sannan yace "wai yaushe suka saba ne haka? Bayan naga ko cikakkiyar wata biyu ba'a yiba". "Hmmm ai waɗan nan ka kalle su Kawai, don nima Babu Yadda banyiba amma ganin abun yafi ƙarfina shiyasa na zubawa sarautar Allah ido, itafa keyi mishi wanka, ita keyi mishi komaima, to ƙarshe ma bari kaji gado ɗaya suke kwana rungume da juna... 😳zaro ido Aayaan yayi "Lallai, ikon Allah, kace abin Babba ne! Shikam Farouk dariya yakeyi Tare Da nuna Hassu yana cewa "Ashe ɗa kika tsinta, to aini danasan da labarin nan da tun tuni Maman SARFRAZ nake ce Miki.. Ɗan murguɗa baki Hassu tayi " ina ruwanka? Ai kai wallahi bakada amana, daga cewa ka taimaka shine zaka wani nemo yan uwan shi, to basai muga wanda zai raba muba. Shima dai sarfraz saiya murguɗa baki sannan yace "ina ruwanka? Ai kai wallahi bakada amana, daga cewa ka taimaka shine zaka wani nemo yan uwan shi, to basai muga wanda zai raba muba. Me Aayaann zaiyi inba dariya ba "aaah Lallai Ashe Hassu tazama role model ɗinshi, wato duk abinda tayi shima sai yayi..... Shi dama Farouk tun tuni dariyar yakeyi, abin kamar a Film.. Guri Aayaan ya samu ya zauna sosai sannan yace "hassun SARFRAZ yanzu ya kikeso ayi to? Ɗan kallonshi hassu tayi Sannan ta wani basar irin ita isasshiyar nan, saida ta ɗauki Kusan minti Uku Sannan tace "kawai mu Yanzu Bama buƙatar taimakon ku, kawai ku tafi ku barmu, inyaso Ni sai in siyar da su gwalbo mukai kuɗin chan Asibitin da za'a yi mishi maganin. Tuntsirewa da dariya Farouk ya kuma yi "wai ke in banda abunki meye Abinda ya shafe ki dashi? Naga ga dan uwanshi ko, to kibari su tafi mana! Ke meye naki? Daɗa ƙanƙame sarfraz hassu tayi "wallahi baku isa ku rabamuba, ina ruwanku damu, kunsan kuna sonshi kuka bari ya ɓace? Shifa Aayaan Abin harya fara sashi tunani, Wato haɗuwar jini ma wata abace kenan, yadda yaga hassu ta dage yasan idan aka rabasu zata iya shiga Wani hali, duba da Yadda shima yaketa fama da damuwar rashin Nawaz Kwantar da murya Aayaan yayi "haba ƴar ƙanwata! Ai ki kwantar da hankalinki domin ƙafarki ƙafar sarfraz, babu Wanda Zai rabaku ko don wahalar da kikasha dashi. Yanzu abinda nakeso shine ki haɗo kayan ki kizo mu tafi tare. Cewa tayi harda bandi amma Koh? "In banda abinki dama ya za'a yi a tafi ba tare da yaya bandi ba? Mota suka shiga Dukansu suka tafi gidan baffa malam, anan Aayaan ya shaida mishi cewa zasu tafi da sarfraz tare da su hassu amma insha Allah ba za'a daɗe ba zasu dawo, domin idan Allah yasa anyi aikin a Sa'a ba za'a wuce wata Uku ba Komai zai daidaita... Da dai baffa malam Yaso ya hana, amma yadda ya gansu duka babu alamun cutarwa sai ya amince amma duk da haka saida yace amanar hassu ya basu, don Allah su kula da ita. Bukkarsu suka koma sannan suka haɗa abubuwan da zasu nema duk da dai Aayaan jira yakeyi su kwasa in anje ya zubar ya sai musu wasu... A mota ne Farouk da Aayaan suka chanza harshe zuwa Turanci, anan Aayaann ya ƙarasa ba Farouk labarin abubuwan da suka faru, da kuma ta inda sarfraz ya zama ƙaninshi... "Lallai wannan Nawaz ɗin Alkhairi ce a gareka, duk dalilinta abubuwa masu kyau sunata faruwa, Allah dai ya daidaita kanku, shi kuma safraz Allah ya bashi lafiya. " Ameen Aayaan yace Tare Da cewa yanzu ya kake gani, in tafi dasu duka gida ne, ko Akwai wata shawarar da kake ganin zatafi? Farouk ne ya kalle shi sannan yace "A nawa tunanin kada ma ka faɗawa kowa ka ganshi, yanzu haka kada kaje dasu gida, mu wuce gidana kawai, ko mummyn ka please kada ka faɗa mata. "Haba Farouk! Meyasa zakace haka? Bayan kasan kowa burinshi yaga sarfraz, kuma kowa damuwarsa a yanzu ita ce a ina za'a ganshi? "Na fahimceka yoo, amma abinda nakeso ka sani shine, a yanzu kowa ya fara cire rai dashi, kuma zuciyar kowa ta ɗan ragu da raɗaɗin rashin shi, to yanzu idan ka kaishi a hakan kasan Dole hankalin kowa zai tashi dalilin ganin halin da yake ciki, kuma ba Lallai idan anyi musu bayani su yarda ba, sannan hakan zai iya kawo delay a tafiyarsu chan England ɗin, gashi irin wannan amfiso ayi surgery ɗin da wuri. Shiru Aayaan yayi "to Shikenan, Allah yasa haka shi yafi Alkhairi, pls zanbar komai a hannunka na arrangements ɗin, ka shirya komai daga kan yin visa har ticket, And kuma ka kira haidar ɗin ka sanar dashi Kafin su isa, wai Farouk Dukansu zasu tafi ko kuwa? Kyalkyalewa Farouk yayi da dariya Sannan yace "ai kai Alhaji ne basuda matsala. "Niba wannan nake nufi ba, shin zasu yarda su hau jirgin sama ma kuwa? Kamanta ko wane masoyi kanyi komai a kan masoyinshi? To naga ai suma masoyane😉! Haka dai sukayi parking a harabar gidan Farouk, ciki Farouk ya kaisu hassu gurin mai dakinshi (Safna), Sannan ya dawo gurin Aayaan dayake yayi-yayi dashi ya shiga ciki, shikuma yace ba zai shiga ba. ATM 🏧 card Aayaan ya mikawa Farouk "gashi duk Abinda ya kamata kayi, pls ka taimaka gobe su samu Flight saboda na ƙosa naga ɗan uwana ya koma dai-dai, pls ko ta online kayi musu bulking da daren nan, yadda zasu samu morning Flight. "To Insha'Allah yoo, komai zaiyi neat kamar kananan, sallama sukayi Sannan Aayaan ya tuƙa motar ya fice daga harabar gidan. Ahankali yake tuki yana tunanin Nawaz. "meyasa zata yanke wannan hukuncin, Ni dai Nasan tsakani da Allah nake ƙaunar ta, ko kaɗan banaso na ganta Cikin damuwa. Haka dai ya Isa gida jikinshi tiɓus, ga farincikin ganin SARFRAZ amma babu halin faɗa, a falour ya tarar da Aseey tana taje gashin kanta. "Bro sannu da dawowa! Ya hanya? Murmushi yayi"hanya Alhamdulillah, ina mum? "Baffa ne ya kirata kuma naga alamun ta shiga damuwa, shine ta shiga ciki ta kwanta.... Babu shiri Aayaan ya nufi ɗakin mumy, domin a nashi gurin gani yakeyi ƙilan Wani abu ne ya faru da Nawaz ɗin shi. Yana shiga yace "mum faɗamin Meya faru? Aunty Aseey tace wai baffa ya kiraki! Ɗago kai mumy tayi "ya kirani son, amma Alamu ya nuna Nawaz bata chan, Domin baffa ma Cewa yayi wai akwai wata goggonta da ta haihu wai in faɗa mata ta kira tayi Mata Barka.... Saboda wai umminta tace wayarta bata shiga kwana biyu.... Wata zufa ce ta karyowa Aayaan, Yanzu yazaiyi, mai ze cewa baffa da ummin Nawaz Idan suka titsiyeshi? "Mummy meye mafita, ko a faɗa Musu ne? "Kul Aayaan, kada ka soma! Ya za'a yi muje gidan Mutane mu ɗauko musu ƴa cikin mutunci Sannan Yanzu kuma mu kirasu muce ta ɓace bamu gantaba? Ai abinma babu hankali a ciki. "Shikenan mum, bari zanyi tunani naga meye mafita, Allah dai ya bayyana ta ... "Ameen dear, kaje kaci abinci, nasan ba Lallai Kaci wani Abu ba. Falour Aayaan ya dawo yanajin zuciyar shi a karye, "shi yanzu ya zaiyi? Ta ina zai Fara Neman Nawaz? Ga rashinta ya fara yi mishi illah, kwata-kwata baya samun isasshen Barci da dare, gashi yayi ta mafarkinta. Zama yayi a kujerar Dake kallon ta Aseey "sis bata gida, meyasa Nawaz zatamin haka? Wallahi sis jinake Kamar zuciya ta zata fashe. Hakuri Aseey taketa bashi, a haka dai ta kwantar mishi da hankali. Miƙewa Aayaan yayi da nufin ya ƙarasa dining ɗon yaci abinci ko babu yawa, ɗon yanzu ba wani iya cin abincin yakeyiba, duk ya faɗa gashi kuma bakinshi yafison taste ɗin abincin Nawaz yanzu. Ƙarar buɗe ƙofar da akayi ne yasa Aayaan waigowa, ai kuwa take ya shamur kamar wanda be taɓa dariya ba, Ashley ya hango _*(yarinyar ƙanin babansu ce, bata jin magana sam, babu kamun kai, Sannan ta likewa Aayaan akan wai ya taimaka ya aure ta)*_ Ko dinning area ɗin be jeba ya buɗe daki ya shige Tare Da Sawa kofar key, don beson Ashley tazo ta dameshi hakakurum ita gata kamar horo, jiki kamar ansawa muciya doguwar riga, sai uban salo da kisisina. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sati daya kenan da tafiyar su hassu London, inda har anyiwa SARFRAZ surgery ɗin, sai dai har yanzu yana process ɗin magunguna, don a ka'ida bazai farfaɗo ba sai nan da 30days, saboda haka tsarin aikin yake, ita kuwa hassu an haɗa ta da matar haidar sai gyara ta takeyi tana koya mata abubuwa, Gashi an samar musu lesson teachers ita da bandi, wannan na tafiya wani zaizo, Kuma babu laifi domin suna gane abubuwan da ake koyar dasu, don Allah ya albarkacesu da budaddiya kwakwalwa, Hassu harta fara sajewa da ƴan kasar, domin madam haidar ta kaita body steaming da Mani cure, harta gashin kanta saiya koma kamar samatashi akayi, domin har wani ƙyalli da sheki yakeyi, kuma dama gashi baƙi. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Zaune Nawaz take a saman dressing mirror, abin duniya Ya isheta, duk rigunan ta sunyi mata kaɗan, Domin idan tasa sai taji ƙirjinta kamar Zai fashe. Kuma Alhali da sunyi mata yawa, siket siket ɗinta ma data sa sai zip ya dare, gashi ita kanta takaanji nauyin jikinta Yanzu ba Kamar da data ke jin kwanta a Iska ba.. Gaban standing mirror ɗin dake Hanyar bayi taje ta tsaya tana ƙare wa kanta kallo, ganin ƙirji ta tayi yayi full Kamar zai fashe, ga hips ɗinta ya daɗa buɗewa sai taga Kamar ba ita ba, domin full figure 8 haka ta koma, ɗan tafiya tayi a gaban mirror ɗin, Aikuwa taga hips ɗinta na sukutur-sukutur. Zare ido tayi 😳😳😳 "nashiga uku! Yaushe na zama haka? Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, a'a, to wannan kibar ta meye? Shiru tayi tana tunani, iya tunanin da tayi babu abinda zatace dalilinshi tayi ƙiba, Abu ɗaya take zargi yanzu :- ~magungunan da inna ke ɗura mata,~ tabbas Akwai alamun tambaya, sosai inna take dagewa akan saitasha magungunan gashi yanzu harda su nonon raƙumi da garin Riɗi take dama mata a Madara tace ta shanye, Tsumi kuwa ba'a magana ga Gumba, anya kuwa? Ni kam kodai Akwai abinda inna takeyi ne? Ga subulan Dilka kala-kala suma.... Hannunta ta kalla taga yayi wani fau, ga taushi da yayi tubus sai ƙyalli yakeyi, har wani damshi-damshi yakeyi alamun cikar Ni'ima a Tare Da ita... Shiru tayi ta zubawa hannun ido "anya kuwa! Allah kasa ba gaskiya bane? (A shirmen Nawaz tunawa tayi sanda Aayaan yacewa Nafisa tanada ciki? Idan kuwa ciki gareni na shiga uku, to yaushe akayi min cikin, to ko Aayaan ya bani Wani Abun da yasa nafita hayyacina ne? To yaushe? Haka ta zama kamar zararriya, daga ta saƙa wannan ta warware saita kuma tufke wancan. Doguwar riga ta samu tasa sannan ta fito falour gurin inna, "Inna wallahi Ni Sai Yanzu na lura da jikina sai naga nayi ƙiba. "Ooh Nawaz wace ƙiba kikayi? Nifa Ban ganiba! Jikinki dai ya murje.. "Inna don Allah ki barni naje gidan Nafisa ƙawata, kinga tunda nazo ban taɓa zuwa ko ina ba, kuma yau kusan kwana na ishirin. Fir inna taƙi amincewa, amma daga baya sai ta yarda ganin yadda Nawaz ɗin ta shiga damuwa, "amma karki daɗe, kuma karki kula Kowa, kuma ki kula da kanki.. Dubu ɗaya Inna ta miƙa mata "gashi kiyi transport da ita. "Inna kibarshi Akwai sauran kuɗi a hannu na, hararar da inna ta zabga Mata ce ta sata amsar kuɗin babu shiri tare da yi Mata godia, ɗaki ta koma ta shirya cikin Wasu riga da skirt, suma daƙyar suka shigeta Sannan ta samu dogon hijab har ƙasa tasa, "inna saina dawo! "Yauwa Nawaz ki gaisheta, Allah ya tsare Adawo lafia. "Ameen" Nawaz tace Tare Da fita daga gidan.... Kasan cewar iska akeyi yasa hijab ɗin duk ya maƙale mata a jiki, sai gyarawa takeyi amma yaƙi yi, gashi taƙi samun abin hawa, duk inna tabi sai maza sun bita da ido, waɗanda suke machine har waige sukeyi. Wani me napep ne nazo wucewa ta gefenta, Aida sauri ta daga hannu tana tsaidashi, ciki ta shiga tana cewa "gaskiya layout zaka kaini. "Okay to Hajiya, amma in zaki bani dama danayi Miki wata tambaya. "Menene fadi tambayarka mana! Ɗan murmushi me napep ɗin yayi "kusan sati Uku da suka wuce na dauko wata daga gaskiya na kawota unguwar nan, kuma wallahi kunyi kama, saidai ita bata kaiki cika ba da haske. Amma kunyi kama matuƙa, shine nace koku Yan biyu ne? "Tab ashe bani kadai naga cikar danayi ba, harda ƴan duniya" Nawaz ta raya a zuciyarya, "Nice mana, unguwar daka daukoni Nan zaka maidani amma ba gidan ba" "Anya zan iya yarda cewa kece ta rannan! Hu'um inkuwa kece ina zargin ke amaryace amma? Murmushi nawaz tayi "Allah Nice kuma single nake banida aure! "Shiru yayi badon ya yarda ba, amma fa abun ya bashi tsoro kwana nawane da zata Zama haka inhar da gaske itace? Har Kofar gidan Nafisa ta nuna mishi Sannan yayi Parking, bayan ta sallame shi ne yace ƙarfe nawa zaki koma in dawo in ɗaukeki? Murmushi Nawaz tayi "inaga wajen ƙarfe Uku yayi, nagode sosai kuwa, saika dawo.. Cikin gidan Nawaz ta shiga da sallamar ta. Galala Nafisa ta tsaya tana ƙarewa Nawaz kallo, "i lallai gaskiya mijinki ya iya kiwo, ji yanda yayi miki ɗure, Kinga yadda kika cika tako ina, ga wani sheƙi da kikeyi, shikuwa meyasa ya fito dake, ai sai ayimai kwace, Kinga yadda kika zama wata ɗanya ɗanya ne, sai kace amaryar da mijinta baya wasa. Ballamata harara NAWAZ tayi "Ni dai kibar wannan soki burutsin naki kizo muje kiji abinda ya kawo Ni. Daki suka shiga tare, ko zama Nawaz batayiba ta cire hijabi "Nafisa nashiga uku, ji Yadda na zama! "Wane shiga Uku? Ai sha'awa ma kika bani, das dake, gaskiya mijinki na kwasar ganima, ko ince kuna kwasa tunda shima da gani jarumi ne. " Dalla! Ni kidena min wannan zancen banzan ki faɗa min mekesa mace ta zama haka Cikin ƙaramin lokaci? Dariya Nafisa tayi Sannan tace "A iya sanina nidai nasan amare ne ke zama haka, saboda sinadarin namiji da yake zuba Musu ance yana yi musu amfani, sai kuma mace mai danyen ciki daga sati biyu zuwa wata uku, to zakiga itama kirjinta ya cika hip ɗinta duk sun buɗe... Toke meye na tambayar bayan kinsan Dalilin da yasa kika zama haka, cikin naki zai kai wata nawa? Miƙewa Nawaz tayi"Allah Nafisa idan kikace zaki ɓatamin rai wallahi zanyi tafiya ta. Da sauri Nafisa ta miƙe "yi hakuri na Dena, ina ogan, naga baki shigo da muhsien ba. "Ni kadai nazo" cewar Nawaz tana kishin giɗa a kujera. "Shikuwa ya barki kika fito a haka, bayan a Yanzu duk namijin dazai ganki a haka saiya haɗiye miyau, balle kuma Yanzu ga ƴan lesbian cike da gari, suna ganin ki ai Shikenan kin shiga uku. Duk idon Nawaz yayi ja, ita yanzuma ta dena zargin inna, ganin takeyi dole Akwai abinda Aayaan yayi mata, Sannan ya ɗirka mata ciki bata saniba, ita Yanzu ya zatayi! Me zatace wa umminta idan ta tuhumeta? "Nafisa don Allah babu wani abu dakesa mace da zama haka bayan abubuwan nan da kika lissafa min? "Gaskiya ban san waniba, iya abinda na sani kenan... Tagumi Nawaz tayi! "Gaba ɗaya ta rasa abinda keyi mata daɗi, ita yanzu ya zatayi ne, me zatayi a rayuwarta indai akace ciki ne da ita? Ta shiga Uku kenan! To amma idan cikine dole na Aayaan ne. Wayarta ta ɗauko ta kunna, tana gama booting message ɗin Aayaan ya shigo, ko gama karantawa batayiba ta maida wayar ta kashe.... *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 50* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Ajiye wayar tayi a gefen kujera tana jin haushin kanta, "danasan zanga wannan message ɗin wallahi da bazan ma buɗe wayar ba, shi dama be manta daniba? Yana chan yana jiran indawo saboda yaci gaba daga inda ya tsaya. Wata zuciyar ce tace "Anya Nawaz bakya ganin yanzu ya kamata ki koma, kinga koda ma Cikin gareki hakanan zai amsa" "Amma Nawaz kin taɓa jin inda mace tayi ciki dare ɗaya? Kuma da Aayaan ya kwanta dake dole sai kin sani sakamakon babu wanda ya taɓa kwanciya dake" abinda kwakwalwata ta faɗa mata kenan..... Ajiyar zuciya Nawaz tayi tana kai kallonta kan Nafisa, Sannan tace "wai ina yaran namu ne? Yauma Bangansuba? "Suna gidan surukaina, kinsan da safe idan zai fita yake kwashe su ya tafi dasu tunda kinga yanzu hutu akeyi. "Allah sarki, yana ƙoƙari shima wallahi. Nawaz tace tare da miƙe kafafuwanta a saman kujera. "Yaushe zaki tafi? Ina fatan dai zaki min yini Koh? "Eh zan jima sai wajen uku za'a zo a daukeni, kinsan a gidan inna talatu na sauka. Shiru Nafisa tayi alamun tunani Sannan tace "wallahi Nawaz ban gane taba! "Inna talatu fa ta hayin ojo, wadda muke zuwa gidanta har muyi wainar fulawa. "Allah Sarki! Cemin zakiyi innarmu, fatan tana lafiya? "Lafia lau take, tanama gaisheki. "Ina amsawa wallahi, inkin koma kice nima ina gaisheta dakyau dakyau don walllahi inna Akwai mutunci. Tashi Nafisa tayi "zakici wainar fulawa in soya mana, Wallahi faɗar sunanta da kikayi sai naji inason ci. Miƙewa Nawaz tayi itama "muje kitchen ɗin muyi tare. (Nikam cewa nayi mayyar girki) °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Aayaann na kwance yana tunani kamar yadda ya maida kanshi yanzu, kullum tunani gashi ya zama so silent, wayarshi ce tayi kara alamun notification ya shigo. Kamar kar ya duba sai kuma Wata zuciyar tace duba mana! Ƙila Alkhairi ne. Janyo wayar yayi a kasalance, ai zumbur ya miƙe ganin message ɗin daya Turawa Nawaz yayi delivering, da sauri yayi dialing ɗin number, Amma switch off. Jiyayi Kamar yayi wurgi da wayar don takaici, komawa yayi ya zauna yana tunanin mafita, so yake yi ya kama Nawaz a hannu don yaci burin rama abinda tayi mishi, amma ta wata fuska daban. Wani shu'umin murmushi ya yayi tare da cewa "yarinya wasa kikeyi dani, amma na wuce da yanda kike tunani, Allah ma yayi zakikai haka kina soyamin zuciya ne shiyasa idea ɗin bata zo mini ba. Wata number yayi dialling, Hello ola! pls ka duba email ɗinka zakaga Wata Number, track The number and send the location details to my email. Komawa yayi ya kishingiɗa yana murmushin cin nasara, yasan Yanzu damuwar shi ta kusa zuwa ƙarshe, tunda anga sarfraz Yanzu kuma ga Nawaz zata bayyana itama... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Zaune Nawaz take a Saman dadduma ta idar da sallar zuhur, zuciyarta tayi nisa a tunani "ko me Aayaan yakeyi Yanzu oho, ina mum da mummy, Yanzu a Wane matsayi suke kallona? Ajiyar zuciyar tayi Sannan ta miƙe tana ninke daddumar. Dayake sai gurin karfe biyu da rabi tayi sallar saboda basu gama wainar da wuriba, ɗan gyara jikinta tayi saboda tasan Mai napep ya kusa zuwa, sosai sukeyin hura ita da Nafisa Anan Nafisa take cewa:- Nawaz don girman Allah ki riƙe mijinki hannun dubu dubu, wallahi samun irinshi a wannan ƙarnin sai an duba, kuma Kinga ga kyau ga ilimi ga kuɗi, to kowannan ya isheki izina, wasu fa zaki gansu zaune gidan mazajen nasu amma walllahi su suke ci da kansu kuma babu Wanda ya sani, balle kuma wadda ta samu ana ci da ita. Kinga kuwa ke Saidai kice Alhamdulillah! Kuɗin fa da Ni kaina ya bani rannan dana ƙirga dubu Talatin da hudu na gani, Kinga ko iya haka aka tsaya Nima ba yagi arziƙi... "Tabbas haka ne, to amma Yanzu Meye mafita?" Abinda NAWAZ ta raya a zuciyarta kenan, sai kuma tace to yanzu fa ya kamata kafin nayi aure nasan inda SARFRAZ yake. Sallama akayi daga kofar gida, ai kuwa nafisa ta tashi ta leka, da sauri ta dawo tana cewa mai ɗaukar kine yazo, "Yanzu rubutamin number ki anan, cewar Nafisa tana mika mata biro da takardar data ɗauka saman fridge. Bayan ta rubuta ne, Nafisa kece wa "to ƙawata Allah ya raba lafiya, sai na kiraki, a gaishemin da muhsien shida baban shi. Ita dai NAWAZ batace komai ba Tunda ta lura Nafisa tayi nisa bata jin kira, duk da dai tasan Aayaan ne yaja mata. Har bakin kofa ta rakata Saida suka tafi sannan itama Nafisa ta koma gida cike da kewar Nawaz ɗin. Hira mai napep yaketa janta ta ita, ita kuma nawaz taƙi sakin jikinta, daga eh sai a'a, kuma dai taga alamun mutumin Babu ruwan shi, sai dai ta lura mayen surutu ne ... Har kwar gidan inna ya kaita Sannan sukayi Sallama ya tafi bayan yace idan zata fita ta duba junction zata ganshi, sai tayi mishi magana zai Kaita duk Inda takeso... Da fara'a Nawaz ta shiga tare da cewa "Inna Barka da gida! Nabarki ke kaɗai Koh? Murmushi inna tayi "a'a Nawaz ai baki ma daɗe sosai ba don hudu fa batayiba har yanzu, ki shiga ki chanza kaya saiki fito kici abinci idan kuma wanka zakiyi to. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° 👀👀👀 London na leƙa Don ganin wace wainar ake toyawa, ai kuwa sarfraz na gani kwance cikin wani dakin Glass an rufe ko ina, alamu ma ya nuna ba'a bari a shiga sai dai idan doctors ne, a cewarsu wai ba'a son hayaniya tayiwa mutum yawa, saboda aikin nasu Zai iya dawowa baya, Hassu na hango sanye da doguwar riga Pink colour ta yafa mayafinta, a yanda hassu ta koma Yanzu da ace banyi dagaske ba Bazan gane taba. Zauna take ta zubawa cikin ɗakin ido, shikuwa bandi Yana tsaye akanta yana cewa "kiyi hakuri hassu in'sha Allah zaiji sauki, ki tashi mu tafi, Kinga tun ɗazu nake miki magana amma kinmin banza... Don Allah kiyi hakuri kinji! In'sha Allah zai warke saurai. Kunnen Uwar shegu tayi, itafa bazata tashi ba, haka kawai ansaka Mutum cikin daki sannan A ki bari kowa ya gansa, Nifa na faraa gajiya, Da bandi yaga abin nata da gaske ne, sai kawai ya samu guri a gefe ya zauna, yana jiran duk sanda ta gama sai su tafi, kasancewar gidan Babu nisa shiyasa ma Madam haidar take bari suke zuwa da kansu wani zubin... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° E-mail ɗin da ola ya Turo mai yake zaune yana dubawa "lallai sweetheart! Ashe tana zaria, hmm Allah ya tona miki asiri, gobe asubanci zanyi na koma Zaria, kuma in'sha Allah bazan dawo ba Saida ke..... Sakayau yaketa jinshi yau, ga Wani farinciki dayake cinshi a zuciya, harya ƙosa goben tayi yaga Yadda za'a ƙare. Shiru yayi da bakinshi be faɗawa Mummy ba saboda kada tace zata bishi, ko Aseey yaƙi fadawa saboda tsaro, yafison sai dai su ganshi da Ita Kamar yadda aka tsara na sarfraz. Bayi ya shiga yayi wanka, kwalliya sosai yayi Saboda farin cikin dayake ciki, tshirt ce fara mai v neck sai wando Blue Black na jeans, sosai kayan suka ƙara fito da kwarjinin shi, ga faffaɗan kirjinshi da damtsenshi (Idan kunsan John Abraham actor ɗin India wanda yayi Film ɗin "Rocky handsome" to sak jikinsu iri ɗaya, saidai Aayaan yafishi kyau a fuska) Yama manta da zuwan wata Ashley, hankali kwance ya fito falourn yana tafiyar shi mai jan hankali don hannunshi ɗaya yana cikin aljihu while ɗayan kuma yana shafa ƙasumbarsa dashi. Ji yayi an rungumeshi ta baya, da sauri ya waiga don Ganin ko waye, Aikuwa idonshi ya sauka a fuskar Ashley sai murmushi take yi mai. Shikam Aayaan saiya ganta kamar dodo, take ya murtuke fuskarshi kamar besan Wani abuba waishi murmushi "ke sakeni!!! Aayaann yace yana tureta Daga jikinshi Sannan ya ƙara da cewa "ke mahaukaciyar Ina ce? Wai so dubu nawa zance kidena taba Min jiki ne? Mumy da aunty Aseey ne suka fito Jin Muryar Aayaan Yana faɗa, "lafiya kake wannan faɗan haka?" Mummy ta faɗa tana kallon Aayaan ɗin alamun tana jiran ya bata amsa.. "Mummy saboda hauka fa ina tafiya shi ne tazo ta rungumeni ta baya, kuma tun kafin jikin ya zama mallakin Nawaz nake ce Mata banaso, amma ita taki bari salon ta kashe Min aure. Tsaye Mummy tayi tana kallon Aayaan, ita kuwa Aseey Sai dariya takeyi, Don tasan halin Aayaan Akwai jisgi kuma ya faɗi hakane don ya ɓata ma Ashley rai. Itakam Ashley kamar ta mutu, duk ta haɗe fuskarta, ta chuno baki da wargajejen laɓɓanta zuciyarta Kamar zatayi bombing..... Yasan mamakin abinda ya faɗa ne yasa Mummy yin shiru shiyasa shima beyi wata wata ba ya fice daga falourn, can garden ya ƙarasa tare da zama a saman wata kujera da aka haɗa ta da katako, wayarshi ya ciro Sannan ya shiga gallery, photunan Nawaz ya nuno yana ƙare mata kallo Tare Da yin wani shu'umin murmushi... "Allah yana sona shiyasa ya bani basirar dazan nemoki cikin ruwan sanyi, wallahi nasha wahalar Rashin ki kusa dani amma komai yazo ƙarshe bi'iznillah.... Wani nishaɗi yakeji Kamar itace zaune a gabanshi..... Ya daɗe a haka Sannan ya koma contact, dialling Number Daniel yayi "Daniel inform your colliques to get ready tomorrow morning by 7am we will travel to Zaria. "Okay sir" abinda Daniel Yace kenan Sannan ya yanke wayar. Number haidar ya kuma kira don yaji ya jikin sarfraz ɗin, Saida suka ɗanyi waya mai tsaho Sannan ya kashe ya kira Farouk, namma dai sun ɗan tattauna Sannan sukayi Sallama. Tunanin Abinda Zai Kai mata yakeyi dukda uban tarin kayan daya jido mata daga Abuja, ga kuma sarƙar Gold ɗinta. Rasa mai Zai siya yayi, sai kawai ya yanke cewa insun fita goben ya duba abin da ya kamata. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Achan gidan inna kuwa, inna ce zaune anayimata kunshi irin ɗan jere, Nawaz ta kafa ta tsare akan itama sai anyi mata. "Ke kam Nawaz Nima da badon bikin da zani gobe ba da bazanyi ƙunshin nanba, kuma nace ki bari idan zaki tafi gida zan kirata tazo tayi miki harda baƙi zatayimiki na Sudan a bayan hannu, Chuno baki Nawaz tayi "Nidai inna don Allah tamini yanzu harda baƙin Wallahi inaso, Kuma idan Zan koma ɗin ma sai a kuma kiranta tayi min sabo" dariya Inna tayi "Shikenan tayi Miki duk wanda kikeso" Ai kuwa Nawaz harda tsallen murna, wayar mai lallen ta amsa tana kallon photunan ƙunshi kala kala a wayar, tama rasa wanda zata zaɓa. Me ƙunshin ce tace "kibari a gama Mata, Ni nasan wanda zan yi Miki, kada ki damu na amare zan Miki, barin gaki fara, nasan idan nayi miki mijinki bazai gane kiba idan kika koma gida. Zaro ido Nawaz tayi, kadafa itama wannan tana zarginta tana da aurene saboda cikar da tayi, sai Kawai tayi murmushi taja bakinta ta tsuke. Inna kam murmushi tayi, duk da bawai tasan Aayaan bane amma tasan Dole idan yaga Nawaz ya ruɗe koda shi ƙarfe ne kuwa. Hankalin Nawaz be kwanta ba har Saida taga an gamawa Inna an fara jera nata, sai murmushi takeyi domin akwaita dason yin lalle kamar aljana. Tunda kinga yamma tayi Yanzu sosai, ja kawai zanyi miki zuwa gobe da sassafe sai nazo nayi Miki flawar Sudan ɗin itama sai in haɗa miki da chilli rani. Murna Kamar Nawaz tayi mene, fuska Kamar gonar auduga, sai washe haƙora takeyi kamar mai tallan MacLean. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Haidar ne wanda fitowar shi daga yiwa wani surgery kenan, yayo hanyar ɗakin SARFRAZ Don ya duba jikinshi, Yadda yaga Hassu tayi zaune lakadan a kasa ne ya bashi dariya, sai kace wadda akaba gadi. Da sauri ya ƙarasa kusa da ita "haba Hafsatul ikraam, kiyi hakuri mana, ɗan naki ya kusa samun sauƙi fa, Wallahi Nayi Miki alkawarin cewa Komai zai zama Kamar ba'a yiba. Shagwaɓe fuska Hassu tayi "Ni so nakeyi na ganshi" murmushi haidar yayi "Idan kika ganshi zaki tafi gida?" Aida sauri Hassu ta miƙe wallahi hardai ka bari na ganshi Allah zan tafi. Gaba haidar yayi tare da cewa to kuzo muje, ammafa kada kuyi magana. "Bazamuyi ba" cewar Hassu tanaji Kamar ansata a Aljannah buɗe dakin yayi suka shiga ciki, abin gwanin Ban tausayi gaba ɗaya kan SARFRAZ an nadeshi da bandage ga Wasu Irin wayoyi da aka jona mishi kala kala, wai nan akwai ta abinci data Iska ta Wadda ke fitar da fitsari da bayangida. Sai dai har wata ƙiba yayi ga haske ɗaya ƙara yi, duk baƙin da yayi a rugar su hassu ya washe ya koma usulin SARFRAZ ɗinshi. Shafa mishi fuska Hassu tayi Tare Da cewa a ranta gashin ƙasumbarsa yayi yawa, Dalilin haka sai ya zama Wani babban mutum. Bandi ma dai sai kallonshi yakeyi yanajin daɗi a ranshi yasan cewa in'sha Allah wata rana SARFRAZ zai koma dai dai, to amma zai iya tunasu kuwa? "To kuzo mu tafi gida, dama na duba ruwan ne, naga zai isa har na dawo, muje gida nima na ɗan samu nayi wanka naci abinci sai in dawo anjima. Rimi Rimi Hassu tabishi Babu ko musu, dama ita burinta taga SARFRAZ, kuma ta ganshi yanzu babu sauran matsala. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Yadda Aayaan ya faɗa haka suka dauko hanya misalin ƙarfe Bakwai, koda Mummy taganshi sanda yake shiryawa ce Mata yayi kiran gaggawa akayi mishi daga NMS Barrack dake Zaria. Sosai tayi mishi addu'oi ita da Aseey, mandiya Ashley kuma sannan ko barci bata tashiba. Ta chan gurin Nawaz kuwa tun shida me lallen tazo, don itama tunda taga Nawaz taji tayi mata har addu'a taketayi azuciyarta Allah yasa su Zama kawaye, shiyasa bata tsaya Wata Wata ba tazo da wuri, tasan Nawaz ɗin zataji daɗi.. Misalin ƙarfe tara har ƙunshi ya bushe an wanke, wai hmm Nawaz kam zama tayi kamar wadda ake daurawa aure yau, farar Fatarta ta amshi ƙunshin sosai sai Wani sheƙi takeyi. Ita kanta hadiya mai ƙunshin Saida na riƙe hannun tana kallo, don gani tayima Kamar bata taɓa yin lalle mai kyan Shiba.. Zuwa lokacin kuwa inna harta gama shiryawa, domin itace ƙirjin biki saboda Yar kanwarta za'a aurar anan Nagoyi (chan cikin Zaria) kuma gobe ne ɗaurin aure. Achan zata kwana, taso suje da Nawaz amma ganin hadiya sai Nawaz tace innan ta tafi su zasuzo gobe tare da hadiya yinin bikin. Mai napep abokinta ta kira har ƙofar gida, saboda Akwai kayayyakin da innan zata tafi dasu, basu suka koma cikin gidan ba Saida sukaga napep ɗin tasha kwana. Sosai suke ta hira da hadiya, don itama a ƙalla zata iya kaiwa ishirin da biyu a shekaru. Wurin ƙarfe Uku da rabi hadiya tace zata tafi saboda zataje tahfiz sai ƙarfe Shida zata dawo, Nawaz tace mata su tafi tare ta nuna mata inda akeyin washing And setting tanaso za'ayi mata straighting ɗin gashinta. Tare suka tafi, Saida hadiya ta nuna mata saloon ɗin Sannan ta wuce makaranta. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Shikam Aayaan sai wajen ƙarfe huɗu ya shigo Zaria, map ɗin motar yasa aka kunna sannan ya amshi tuƙin saboda yanaso ya kula sosai, location ɗin da ola ya Turo mai yake tabi ahankali. Mamaki Abin yaketa bashi sanda yaga layin su sarfraz yake nuna mishi, ai kuwa yaci gaba da kallo yana bi, sai kuma yaga ya chanza hanya, a daidai gidan nafisa yaga locator ɗin ya tsaya. Shiru yayi yana kallon gidan domin Kamar ya taɓa ganinshi, da sauri yace "gidan nafisa kawarta" Fitowa Daga motar yayi yanayin Wani shu'umin murmushi "Daniel pls go And knock the door" Ƙarasawa Daniel yayi ya ƙwankwasa kofar, ba'a jima ba saiga yaro ya fito yana kallonsu. Kiranshi Aayaan yayi "maminka tana nan? "Eh tananan" yaron yace yana kallon Aayaan. Kaje kace mata wai mijin Aunty Nawaz yana waje. Aida gudu yaron ya kwasa ya shiga gida, ba'a Fi minti Uku ba saiga Nafisa ta leko sanye da hijabi. Murmushi tayi ganin dagaske Aayaan ne "ina ƙawar tawa? Tambayar da tayi sai da Aayaan yaji zuciyarshi ta buga, Kada dai ace bata nan ma! Muryar Nafisa ya jiyo tana cewa "yi hakuri bamu gaisaba, ina yini, yasu inna? "Lafiya Lau Alhamdulillah ya yara" Murmushi Nafisa tayi"yara suna lafiya, ina muhsin? Ko yana gurin inna? Ashe a gidan inna kuka sauka? Wani daɗi Aayaan yaji ganin bema tambayetaba ta sashi a kan hanya, (mutum Idan ya cika surutu sai dai a barshi) Ai kuwa suna chan gidan inna, dayake Ni banma je gidan innan ba tafiya ta kamani, to Sai yau na dawo kuma nakira Number mutuniyar taki bata shiga ba, gashi Bansan gidan innar ba shi ne nace kila Idan nazo zaki Iya kwatanta min! Washe baki Nafisa tayi, jin cewa Aayaan zai iya Neman taimako a gurinta "aikuwa dai inna tana hayin ojo ne, idan kasan makarantar commercial to gidansu Yana gefen dama, da dai sanda muke zuwa Blue ɗin fenti ne, amma dayake an Dade yanzu bansan wane kala bane. Hannu Aayaan yasa a aljihu ya ciro sabbin yan ɗari Biyar Biyar ya mikawa yaron Nafisa, Sannan yasa Daniel ya ciro kwalin chocolate a boot ya bashi, sai godia Nafisa takeyi tana cewa "baka gajiya, to Allah ya saka da alkhairi, Idan kaje kace ina gaida su, Allah ya tsare hanya. Locator app ya shiga yayi searching ɗin ojo commercial, ya saita suka ɗauki hanya. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Hajiya Nawaz na zaune shigowarta kenan daga saloon tayi wanka, sam bakinta babu daɗi ta kuma rasa me zata ci gashi batason fita waje, miƙewa tayi ta ƙarasa katangar gidan dake haɗe dana inna, Sallama tayi Sannan tace mamii don Allah Abba yayanan, tachan gidan mamii tace eh yananan inturoshine? "Eh dama zan ɗan aikeshi shago ne" "To gashinan zuwa" cewar mamii Godiya Nawaz tayi Sannan ta juya zata koma tsakar gida don jiran shigowar Abba. Binta nayi da kallo, don wata riga ce play a jikinta doguwa, gata rubber, duk tabi jikinta ta liƙe Sannan kanta babu ɗan kwali sai dai parking ɗin gyararren gashinta da tayi. Da gudu Abba ya shigo yana dariya, "ina wuni Aunty baturiya" Yaron Yana sonta sosai domin ƴar baturiya ma yake ce mata, gashi kuma Duk sanda ya siyo mata Abu Shima saita bashi nashi, shiyasa duk sanda ta kirashi yake zuwa da gudu. Kuɗi ta miƙa mishi "Abba don Allah chocolate Zaka siyo mini a shago, Irin Yar ɗari ɗari ɗin nan guda goma. "To Abba yace Tare Da yin hanyar soro Don fita daga gidan. Ɗai ɗai Nan Aayaan sun iso layin yama fito Daga cikin mota yana Bin gidajen da kallo, rasa wanne ne gidan inna yayi Ganin gida Kusan biyar Duk da blue ɗin penti. Da gudu Abba ya fito yana murmushi don yasan Idan ya siyo Shima zata bashi. "Abokina zo" Aayaan yace yana ɗaga wa Abba hannu alamun dashi yake. Karasowa Abba yayi Sannan Yace "Ina wuni" "Lafiya Lau abokina, don Allah ko kasan gidan Inna acikin gidajen nan? Da sauri abba yace"inna wadda baturiya tazo gurinta? "Ya sunan baturiyar" "Sunanta aunty Nawaz, itace ma ta aikeni na siyo mata chakuleti yanzu, amma fa ita innar bata nan. Murmushi Aayaan yayi Sannan yace"ina innan tajee? "Ɗazu ta shigo tayiwa mamii sallama wai zataje biki cikin Zaria kuma wai kwana zatayi.. "Okay, gidan daka fito shine gidan innar ko? Ɗaga Kai Abba yayi alamar eh, hannu Aayaan yasa a aljihu ya ciro sabbin yan ɗari Biyar ya mikawa Abba Sannan yace ya tafi gida Kada ya siyo, shine mijinta ta kuma ya siyo mata, dubu ɗayar Abba ya mikawa Aayaan Sannan Yace"ga kuɗin to kakai mata, "Nabar maka" har Abba ya ruga Zai tafi Aayaan ya tsayar dashi, kwalin chocolate yasa Daniel ya ciro ya bashi. Kallon securities ɗin Aayaan yayi Sannan yace "ku tafi da motocin amma ku bar min wannan, yana nuna wadda tsarabar Nawaz take ciki, zamu haɗu gobe in'sha Allah." Kofar gidan Inna Aayaan ya karasa ya tsaya, Sannan ya Fara knocking a hankali, Nawaz Dake zaune jin ana Knocking Sai ta zata ko Abba ne ya dawo, dayake kofar takan rufe kanta sai Kawai ta tashi don zuwa ta buɗe. Aayaann ta gani tsaye yana Mata wani irin shu'umin murmushi, ji tayi Kamar ta maƙale a gurin, domin kasa motsi tayi, mamaki haɗe da tsoro ne suka mamaye ta lokaci guda... Shikuwa Aayaan Binta yayi da kallo tun Daga kanta har zuwa ƙafa, Sannan kuma ya koma sauran sassan jikinta, gani yayi Kamar ba Nawaz ba, mamaki yake yi wai dama haka take ko Kuma Yanzu ne ta zama haka? Ai da sauri ya tafi don ya rungumeta koya samu sauƙin abinda yakeji a zuciyarshi, ita kuma Nawaz ganin ya nufota Sai taji wani ƙarfi ya shigeta tayi Cikin gidan da gudu tana cewa "Inna za'a Shigo Miki gida!. Har Cikin falourn Aayaan ya bita yana cewa "wace innar kuma? Ko guda biyu ne innar, naga dai Inna ta tafi Zaria Koh? Jin haka da Nawaz tayi Sai taji cikinta ya ƙulle, ai babu shiri ta Fara ja da Baya tana Cewa "ya Aayaan don Allah ka tsaya ka saurareni please! Shikam nufarta yayi da sauri don so yake yajita ya jikinshii, yaji duminta don yayi mugun missing ɗinta, ga kuma Yadda yaga ta koma duk motsi daya sai duka jikinta ya motsa...... Allah kuyi comment da sharhi, inba haka ba inbarku zuwa sabuwar shekara sai mu cigaba. 😉😉 Ƙaƙaƙara ƙaƙa ga Nawaz ga Aayaan 😳😳🤔. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *Episode 51* *Na Hafsat Aliyu Shuaibu Chikaji ✍️* Yadda yaga Nawaz ta ruɗe Kamar taga dodo ne yasa ya tsaya a Inda yake "sweetheart wai meyasa kike mugun jin tsoro nane, ji abinda kikeyi fa, sai kace kinga dodo" Itama Nawaz sai taji kunya ta kamata, ɗan natsuwa tayi kaɗan amma kanta na kallon ƙasa. Hakan da tayine ya ƙara ba Aayaan damar daɗa ƙare mata kallo, Lallan kafarta dana hannunta yakebi da kallo, Aayaan yanason lalle sosai, saboda yasha taya Mummy idan zatayi, kuma Bayan tayi yaita kallonta yana Cewa tayi kyau... Maida kallonshi yayi kan hips ɗinta, "a'a to wai da wauta ce tasa banma San yadda takeba ko kuwa? Sosai hips ɗin ya baje a cikin doguwar rigar, har wani ɗan tudu yayi daga gefe, koda yakai idonshi kankirjinta nanma dai zare ido yayi... Gashin kanta kuwa har wani ƙyalli ƙyalli yakeyi, wani irin Abu yaji ya tsirga mishi, gyaran murya yayi Domin jin Muryar tashi yayi Kamar ta dishe "sweet heart meyasa kika gudu kika barni da ciwo a zuciya ta? Kinsan da gaske Ina sonki kuma ina ƙaunarki..... Ɗan ɗago da Ido Nawaz tayi da nufin ta saci kallonshi, ai kuwa charaf suka hada Ido, Anan ne yaga usulin Khan da Nawaz tayi.... Da ɗan sassarfa ya ƙarasa kusa da ita, ɗaga ta sama yayi sai yaji ta ƙara Nauyi fiye da da, "Sweet love me Inna take bakine kika Zama Yar lukuta? A hankali ya sauketa sannan ya haɗa ta da kirjinshi ya rungumeta, a yanda yakeji a zuciyarshi da ace zai iya fasa ƙirjin shi ya sata a ciki da Hakan zaifi yi mishi daɗi, hannun shi ya zagayo yayi wrapping a ƙugunta, gaba dayansu bugun zuciyarsu saiya tsanan ta kuma a tare jikinsu ya bada wani Ni'imtaccen dumi da kamshi.... Shiru Nawaz tayi tana sauraron bugun zuciyar Aayaann, amma zuciyarta Fall tsoro kasancewar ta ita kaɗai kada Aayaan yayi mata wani abu.. Ƙasa yayo da Fuskarshi dai dai saitin kunnenta yace "please dear ki bani dama just one kiss. Namma dai Nawaz shiru tayi tana sauraron shi, bataso tace zatayi mishi Musu, domin Babu maceci sai Allah, ajiyar zuciya tayi haɗe da furzar da numfashi mai ɗumi daga bakinta "yaya Aayaann pls ka sumbaci goshina kawai. "Nop mouth To mouth Nidai nakeso, a taimaka min pls. Sannan ya daɗe haɗe ta da jikinshi sosai..... Wani irin Abu Nawaz keji yana bin duk illahirin jikinta (tsumin inna ya Fara aiki 😉) ga wata uwar kasala data saukar mata nan take, gaba ɗaya ta ƙasa yin wani kataɓus,. Aayaann kam ji yayi tsayuwar tayi yawa, ga duka gwuiwowinshi sunyi weak, Kujerar Inna ya ƙarasa ya zauna tare da tattare Nawaz zuwa saman cinyarshi, Sannan yayi cuddling ɗinta, yau kam Nawaz ta bashi mamaki domin sam babu wannan tsiwar Tata, tayi shiru kamar Ruwa ya cinyeta.... Ita kuma Nawaz addu'a takeyi a zuciyarta akan Allah yasa hadiya ta shigo, kila Aayaan ya rabu da ita. Sun daɗe a haka Kafin daga bisani Aayaan yace "an bani dama?" "Pls kayi hakuri don Allah, baka faɗamin ina Mummy da aunty Aseey suke ba, da muhsien ma da kuma Mummyn SARFRAZ! "Dukansu fushi sukeyi dake kuma sunce babu ruwansu dake tunda baki daukesu a komai ba. Wani iri Nawaz taji har zuciyarta, tabbas bata kyautaba Amma ai Aayaan ɗinne ya hanata saƙat, kuma ya riƙa bata kunya. "Ki shirya abinda zaki faɗa Musu idan mun koma, Domin ƙafarki kafata tare zamu koma in'sha Allah. Fargaba ce ta kama Nawaz Lokaci guda, ita batasan me zatace Musu yasa ta gudu ba, kuma bazama ta iya kallon suba "ummina tasan bananan? Ɗan murmushi Aayaan yayi "hmm ai ummi ma cewa tayi ta cire hannu Babu ruwanta dake, wai kin nuna basu isa dakeba... "Wallahi yaya Aayaann duk kai kaja min wannan abun, nace maka kadena taɓa min jiki amma kaƙi, kuma saboda Rashin ta ido ma a gaban Mummy fa ka fito dani daga dakinka, baka tunanin suyi wani tunanin. "Mummy na tasan halina kuma ta yarda dani hundred percent shi yasa ma bata haufi Idan taga nayi abu... Shiru Nawaz tayi tana tunanin yau dai gata gashi kuma Babu kowa a gidan, juyo da fuskarta yayi dai dai tashi sannan yace "can i? Rufe idonta tayi tana girgiza kai alamun a'a, sannan tace pls kayi hakuri it's Haram and Idan na Barka anything can happen. Yadda tayi maganar tana motsi da laɓɓanta a hankali yasa Aayaan saurin haɗe bakinsu waje ɗaya, sosai yace yawo da harshen shi cikin bakinta tare da sucking ɗin laɓɓanta passionately. Zaro ido Nawaz takeyi tare da mutsu mutsu, amma ta kasa koda motsa hannun Aayaan daga jikinka saboda ba ƙaramin riko yayi mata ba, daga yadda yake kissing ɗinta tasan yau mai kwatarta sai dai Allah, gashi Babu bakin Magana balle ta roke shi. Wasa wasa taji yana bin sassan jikinta da hannun shi, bata ankara ba sai jin hannunshi tayi a kirjinta yana ƙoƙarin zame mata bra, duk iya karfinta ta haɗa ta shurashi amma ko gezau Aayaan beyiba saima ji tayi kamarma ƙara kiketa yayi, gashi yaƙi sakin mata baki balle ko ihu ta samu tayi. Hawayene Kawai yake zuba daga idonta, ga zuciyarta data karye, Babu Abinda yake mata yawo a kwakwalwa illa Maganar umminta, "(Nawaz kiji tsoron Allah, ki riƙe mutuncinki duk rintsi kada ki yadda ki saki budurcinki a titi, duk wanda zai miki daɗin baki Wallahi yana samun abinda yakeso ya dena kallonki da mutunci, kuma kiyi aure namma miji ya rainaki, shikenan fa rayuwaraki ta shiga garari,) Sosai Aayaan ya fita daga hayyacinshi, ƙoƙarin zame mata riga yakeyi, itakuwa ta rike rigar gam saboda tasan Idan ta bari ya raba ta da rigar Shikenan ƙaryarta ta ƙare. A hankali ya cire bakinshi daga nata ya maidashi gefen wuyanta yana kissing, sosai bakinta yakeyi Mata zuci gashi tama kasa magana, domin ji tayi Kamar an yanke mata harshe.... Chan dai dataga Abin Aayaan bame ƙarewa bane sai ta fara Magana duk da Muryar Tata a dishe take, "yaya Aayaann don darajar Annabi kada ka keta Min haddi, wallahi idan ka kusanceni saina kashe kaina, domin nasan ummina tsinemin zatayi, amma Idan kaga hakan shine dai dai nina haƙura. Ko kaɗan Aayaan be kula taba illah ma ƙara kaimi da yayi a abinda yake yi, Babu inda hannun Aayaan be kaiba a jikin Nawaz, musamman kirjinta donji takeyi ma kamar barkono aka shafa mata saboda zugi, can dai taji yayi mata wata irin wawuyar runguma tare da kama kwankwasonta yana matse wa da nashi Kamar zai karyata, sai kuma taji ya saketa a hankali yana sauke nunfashi da sauri da sauri. Hannunshi ya haɗa ya sargafe da nata yana matsawa kaɗan kaɗan. Kamar me koyan magana ya fara jera kalmomin bakinshi "I'm sorry sweetheart, Wallahi bazan taɓa yi miki doleba, i have That feelings for women, ina tausayin mata kuma ina baƙin ciki yau ace gashi anyiwa wata fyaɗe, Kinga kuwa tunda bakyaso idan na sake nayi to ya Zama nayi miki fyaɗe kenan. Kuma idan hakan ta faru Ni kaina bazan iya yafewa kaina ba. I love You! I Love you!! Idan nace i love You Ina nufin i Love You ɗin dagaske... Nawaz ina ƙokari akanki sosai, wallahi ban taɓa Ganin macen da Idan na ganta ba take ƙara tabbatar min da cewa Ni namiji bane sai ke, duk yadda nakai da daurewa amma sai kin cini yaƙi, i am sorry once again. And kuma kece gaba ɗaya kin ƙara chanzawa, tunda na ganki na rasa natsuwata har ji nayi kamar numfashina zai ɗauke ida banjiki a jikina ba. Idan da kinsan irin tanadin danayi mana a first night ɗinmu da baki wahalar da kanki Wajen bani hakuriba, don nayi Wa kaina alkawarin cewa sai kinaso inaso, That means duka munaso, and Will make it unforgettable for both of us, domin Anan ne zan fito miki da usilin ƙaunar da nake yi miki a fili. Fatana ɗaya shine kema ki soni Don Allah, abu na biyu shine don Allah kidena jin tsorona pls. A yadda akasan masoya shine duk sanda ɗaya yaga ɗaya farinciki ne ke bayyana a fuskarshi, amma Ni duk sanda kika ganni babu abinda nake gani a Cikin udanunki face tsantsar firgici da tsoro. Tunda ya fara magana tana sauraron shi, tabbas Aayaann soyayyar Gaskiya yakeyi mata domin gejin da yakai ba kowane namiji bane zai kai wannan gejin kuma ya rabu dake salin alin ba, kuma duk abinda ya fada Gaskiya ne Domin ita kanta shaida ce, saboda sanda suka haɗu a daji koda wasa be taɓa yunƙurin taɓa mata jikiba, sai yanzu da suka chakudu da juna. Hamdala taketayi a zuciyarta da Allah yasa har Yanzu tana nan a matsayin ta na budurwa, don a yanda zuciyarta ta karaya bata taɓa tunanin Aayaann zai rabu da itaba. Haƙiƙa taji daɗi da Allah yasa Aayaann nada hangen nesa, girmanshi taga ya Karu a idonta sosai, ga kuma wata Irin kunyarshi dataji ta rufeta. Yanzu fa ko hijab tasa kenan a banza tunda babu inda be taɓa ba ajikinta, itakam yazatayi da wannan Abin kunyar? "Inna batada da yara ne? Aayann yace yana komawa gefenta.. A hankali Nawaz tace yaranta uku, biyu mata ɗaya na miji, su matan sunyi Aure namijin ne Karami shi beyiba tukuna. "To miji fa" Aayaann ya kuma jefo mata wata tambayar. "Tanada shi amma yana Niger tare da ɗan innan, saboda tacemin Tare sukaje ganin gida shine ta barsu acan ita ta dawo... "Allah sarki! Allah ya dawo dasu suma lafiya" cewar Aayaan yana kai hannunshi saman side table, purse ɗin dake ajiye ya dauko Tare Da zage zip ɗin, ƴan dubu daya ya gani guda takwas sun zubo mishi, murmushi yayi Sannan yace yau Kuma ruwan kuɗi akeyi kenan. Ita dai Nawaz bata kula shiba, ita jirama takeyi ya ɗauke kafarshi daga jikinta ta tashi ta gudu amma yaƙi. "Purse 👛 ɗin waye Wannan?. "Tawa ce" cewar Nawaz a hankali "Ashe ke hajiya ce, to nawa za'a bani a ciki?. "Nima fa Inna ce ta bani dubu goma da zata tafi, tace in dauki dubu biyar ko zan sayi Wani abun, dubu biyar ɗin kuma wai wata zatazo ta amsa.... Ɗan murmushi yayi " to in dauki dubu daya aciki? Cewa tayi "ko duka ka ɗauka ma Babu komai" Sosai Aayaann yakejin daɗin hirar da sukeyi, amma kiran sallar dayaji ne ya tayar mishi da hankali, kenan isha'i tayi gashi basuyi magrib ba, da sauri ya miƙe Tare Da cewa ina bayi muyi wanka! Itama miƙewa tayi ta kwasa da gudu ta shige bayin Tare Dasa sakata, " wane irin muyi wanka, hmm ya Aayaan da gaske yake yi, nikam bazan iya wannan abin kunyar ba Wallahi. Dariya yaketayi don ta bashi dariya sosai, kuma childish behavior ɗinta yana birgeshi, fita daga faloun yayi zuwa tsakar gida. Sosai gidan ya burgeshi, ɗan daidai kuma daga ganinshi na Masu matsakaicin ƙarfi ne, ko ina tsaff a gyare, sam Babu kazanta a Cikin gidan. Kofar dayaga alamun kitchen ne ya nufa ya shiga, buhun coal yagani a gefe ga kuma sauran kayayyakin amfani suma a shirye suke tsaff. Ashanar daya gani a saman table ya dauka don so yake ya hura wuta ya dora Musu Ruwan wanka don garin Akwai sanyi, yasan koda shi Zai iya yi dana sanyi ita bazata iya yi ba. Tukunya dake kan mangal ɗin ya kama da nufin ya sauke ta ƙasa sai yaji da zafi alamun akwai Abu a cikin ta, buɗewa yayi yaga Ruwan zafine cike alamun ya tafasa har ya gaji. Tsakar gida ya fito ya ɗauki bokiti ya juye Ruwan Sannan ya dauka ya nufi falourn don kaiwa Nawaz, ganinta yayi ta shige bayin da sauri hannunta riƙe da Flask ɗin Ruwan zafi. Murmushi yayi sannan ya fita zuwa bayin tsakar gida, shima bayin tsaff dashi sai kamshin IZAL yakeyi. A gurguje ya watsa Ruwan Sannan ya kama gefen wandon shi inda ya bata ya wanke Sannan ya maida Kayan jikinshi tare da fita daga bayin. Yana shiga faloun ya tarar itama Nawaz fitowarta kenan, sanye take da hijabi amma yadda yaga fuskarta jike da ruwa ga sajenta da gashin goshinta sun kwanta sunbi jikin fuskarta saboda ajike suke. Murmushi yayi jin alwalarshi ta karye, "dama nasan za'a rina, dole fa na ɗauki mataki wallahi, don inba haka ba kwaɓa ta zatayi ruwa. Da anashi yaso ya jasu jam'i ne amma yanzu ya sadakar yasan bazaima iyaba. Cewa yayi ɗan bani dadduma, da sauri ta ɗauka a inda ake ajiyewa ta tawo kawomai, rintse ido yayi Ganin yadda jikanta yake zuyawa a cikin hijabin. Yana amsar daddumar yayi waje da sauri, buta ya ɗauka ya tari ruwa Sannan ya shiga bayi, bayan ya fito ya daura alwala ya tada sallah. Addu'oi sosai yayi wa Ubangiji na nuna mishi Nawaz da yayi Cikin sauƙi ba Tare da Wata dabara tashiba, a hankali ta mike ya nufi kofar faloun ya daga labule, dinɗin yaga ɗakin kasancewar Garin yayi duhu, "sweet heart pls kizo ki rakani anguwa! Nawaz tana zaune cikin dakinta ta jiyo shi, a hankali ta tashi jiki Babu laka Sannan ta fito falourn ta nufi Hanyar kofar, tare suka fita daga gidan zuwa kofar gida. Da sauri Aayaan ya zagaya ya buɗe Mata kofa, Saida ta shiga sannan ya mayar ya rufe tare da zagayawa shima yana shiga gefen driver. Koda ya zauna ita ya kalla yace "inane Hanyar titi? Da hannu Nawaz ta nuna mishi don ita gaba ɗaya kunyarshi takeji kamar ta ruga a guje haka takeji. Saida suka fita titi Sannan ya kuma ce mata "ina zan samu store ɗin magunguna" "Kayi gaba muje idan anzo gurin zan nuna maka, "alright thanks" cewar Aayann yana ci gaba da tukin sa... Sunyi tafiya sosai sannan yaji shirun ya isheshi, "sweet heart babu ko ƴar hirar soyayya? Namfa garin kune ya kamata ki riƙa nunamin gurare kina faɗa Min sunan su amma kinyi shiru. "Yauwa ga pharmacy ɗin" Nawaz tace da sauri tana nuna gurin da yatsanta ta jikin glass don ta katse Maganar da yake yi.. Parking ɗin motar yayi sannan ya fita daga motar ya shiga pharmacy ɗin, ba'a fi minti Bakwai ba ya fito riƙe da wata ƙaramar roba a hannunshi. Saida ya shiga motar ya zauna Sannan ya buɗe robar tare da zazzago wasu ƙananun kwayoyi guda biyar ya watsa a bakinshi, Ruwan dake ajiye a gefe ya dauka ya ɓalle murfin Sannan ya kafa kai, saida ya shanye ruwan tukuna ya cire robar a bakinshi ya jefata waje. Ita dai Nawaz tana zaune tana kallonshi... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Yauma Kamar kullum hassu ce zaune a bakin ɗakin SARFRAZ tayi tagumi Tare Da zubawa ɗakin idanu, sam bata gajiya da zuwa Asibitin, har likitoci sun gane ta, dasun ganta zasu Fara tsokanarta suna dariya. Gani tayi Kamar SARFRAZ yana motsi, ai babu shiri ta mike ta karasa kusa da Glass ɗin tana kura ido don Ganin da gaske ne ko kuwa gizo ne, saboda ance sai nan da sati biyu ko uku zai tashi.. Ai kuwa da gaske motsi yakeyi, ko Bandi bata tsaya fadawa ba ta nufi cikin asibitin tana Cewa Wallahi motsi yakeyi kuzo ku gani, ganin yadda ta kwasa a guje shima sai bandi yabi bayan ta. Kicibis yayi da likitan da yakeda shifting yau Tare Da Hassu tana cewa, Wallahi motsi yakeyi da harshen Hausa, don tama manta cewa da Bature take magana. Sauri sauri gudu gudu suka Isa dakin, ai wani uban ihu da hassu ta zabga Saida likitan ya toshe kunne Tare ta Saurin kallon Inda SARFRAZ yake kwance. Jinine yake fita ta hanci ta baki babu kakkautawa.... Likitan ne ya ƙarasa da sauri ........ *AYAAN YA SAMU DAMA AMMA BEYI ANFANI DA ITA BA, TO KO DAI RABON SARFRAZ CE DUK DA DAI GASHI CHAN RAI KWAKWAI MUTU KWAKWAI* INA JIRAN SHARHI *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *52* *NA HAFSAT ALIYU SHUA'IB CHIKAJI* ✍️ Likitan ne ya ƙarasa da sauri tare da tallabo sarfraz da hannunshi sannan ya ɗago kan gadon yadda kan SARFRAZ ɗin zaiyo sama, wayoyin dake jikin kan SARFRAZ duka ya cire Fuskarshi kunshe da murmushi. Hassu Wadda tun tuni take rusa ihu sai Sannan ta Kalli bandi "bandi kalli fa, wallahi murmushi yakeyi, ace mutum yana aman jini amma yana dariya, gaskiya turawan Nan basuda imani.... Kusa da shi bandi ya ƙarasa tare da cemishi "likita meya faru, naga kana murmushi!" Cikin ɗan turancin daya fara iyawa a gurin masu yi musu lesson. "Aikinne yayi kyau sosai, kaga wannan jinin daya amayar shine wanda ya maƙale mishi a cikin kwakwalwa kuma da wanda ya zuba a ƙirjin shi dalilin harbin da akayi mishi, yanzu haka muna saran a kowane irin lokaci zai iya farkawa" bayanin da likitan yayi wa bandi kenan da turanci. Hassu taɗan fuskanci me likitan yace, amma tana buƙatar ayi mata bayani sosai. "Bandi naji kamar yana cewa aikin yayi kyau?" "Eh haka yace kuma yace wai daga yanzu zai iya tashi ko Wane irin lokaci" Dadine ya cika Hassu ta tafi da gudu ta rungume bandi "yaya bandi Allah yasa idan ya farfaɗo kada yace be sanmu ba! "Ameen" bandi yace tare da bubbuga kanta a hankali. Duk da kasancewar yamma tayi sosai har garin ya Fara duhu amma asibitin fayau yake da haske Kamar Rana dalilin futilun da suka cika yalwataccen harabar asibitin da haske, Tuni aka kira haidar yazo shima sai murmushi yakeyi Domin yasan idan Aayaan yaji wannan gagarumin labarin abotarsu zata ƙara ƙarfi Fiye da yanzu. Ya kira wayar Aayaan yafi so hamsin amma taki shiga, "shiru yayi Sannan yace"bafa Wani tazarar lokaci garemu sosai ba, balle ince ko dare ya raba ne, nasan Yanzu bazai wuce ƙarfe tara da wani abuba, amma kila Akwai abinda yake yi ne wanda beson hayaniya. Farouk ya kira ya sanar mishi Sannan yacewa su Hassu su Wuce su tafi gida, fir Hassu tace ita batasan zance ba, wai bazata tafi ya tashi Babu kowa a kusa dashiba. Duk yin duniya haidar yayi amma Hassu ta shafawa idonta toka tace Anan zata kwana, Ganin haka da haidar yayi sai yace wa bandi ya zauna su kwana tare. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Tada motar Aayaan yayi Tare Da kallon Nawaz yana murmushi "me zakici in siyo Miki?" "Babu komai" Nawaz tace a hankali. "Au nama manta, duba back seat ga tsarabar ki nan, maybe ki samu Wani abu da zaki iya ci, hope tsarabar batayi miki kaɗan ba? Bayan Nawaz ta waiga, ganin kwalaye tayi jibgi amma kuma wai ahaka ne yake cewa ko sunyi kaɗan! "Lallai ya Aayaan " abinda ta raya kenan a zuciyarta. "Akwai wasuma a boot duk nakine" murmushi ya Kuma yi mata, "Sweet love kinƙi yi Min magana, ko kina fushi da nine? Murmushin yaƙe tayi "a'a bana fushi dakai, amma kayan ne naga kamar sunyi yawa, Bansan ya zanyi da suba. "Komai nawa nakine, Wannan kaɗan ne daga cikin abinda zan iya yi Miki. Ayanda nake ƙaunarki wallahi Zan iya mallaka Miki komai nawa... Mamaki maganar Aayaan taba Nawaz, wai shi meyasa komai yake daukarshi a matsayin wasa ne? "Ya za'a yi yace zai iya mallaka min komai nashi?? "Nasan wannan shurun da kikayi kina kokwonto ko wasa nakeyi Koh? To wallahi da gaske nakeyi, ko haufi kada kiyi.. "Nagode sosai, ALLAH ya ƙara girma!". "Ameen dear, amma da cewa kikayi Allah ya bani ke da nafi farinciki... Murmushi Nawaz tayi batare da tace komai ba... Bayan sun isa kofar gidan Inna yayi Parking Sannan ya daukar mata kwalin chocolate da na caramel suka shiga cikin gidan, falour ya ajiye sannan ya koma ya rufe ƙofar gidan saboda dare ya riga yayi. Kafin ya koma harta kunna haske a dakin, sannan ta dauko warmers guda biyu ta ajiye a Saman table.. Murmushi yayi "me aka tanadar min? "Tuwon alkama ne da miyar riɗi" "Wow Masha Allah, Gaskiya naji daɗi bari nazo naci, wanko hannu yayi sannan ya sauko da kulolin ƙasan carpet inda ya zauna, budesu yayi Tare dayin Bismillah yana fara ci, sosai ya maida hankali yake cin Tuwon kuma da Alamu yayi mishi daɗi... Kallonta yayi "gaskiya kin iya abinci sosai, randa na fara cin abincinki Saida nayi overdose, Gashi yanzuma zakisa nayi kuma kinsan darene babu kyau cin Abu ne nauyi da yawa. "To kabarshi haka sai in Kawo maka zobo ka sha, Nawaz tace Tare Da ɗauke kular daga gabanshi. Murmushi yayi "shine kika ɗauke baki bari na ƙara kadan ba? Ita dai gaba tayi ta ajiye kular a gefe sannan ta dauko mishi jug ɗin da zoɓon yake ciki ta dawo gabanshi ta ajiye.... Godiya yayi mata tare da buɗe jug ɗin yana kafa kai, namma Saida ya kusa shanye wa Sannan ya cire jug ɗin daga bakinshi yana cewa "wai sweet heart komai kin iya ne? Gyara zama yayi ya miƙe kafafunshi dakyau sannan yace "bari abinci ya ɗan saukar mini sai muje mu kwanta. "Zaro ido Nawaz tayi"mu kwanta fa kace? Wai kana nufin Tare zamu kwana? Murmushi Aayaan yayi "just trust me for today only, namiki alƙawarin babu abinda zai faru. "Damuwar data fita daga ciki ce yan mintocin da suka gabata ta dawo mata sabuwa, koma ince tafi tada. Amma abin mamaki koda ya dauke ta suka kwanta a cikin dakinta tasan dai ya rungumeta a jirgin shi amma ko kaɗan babu abinda yayi yunƙurin yi mata, tanajinshi yayi barci, sai Sannan itama barcin ya dauketa. Misalin ƙarfe huɗu da rabi ya tashi, kitchen ya shiga ya kunna wuta Sannan ya ɗora ruwan zafi, koda ya tafasa ɗaki ya koma ya dauko Flask a Saman tables ɗin Inna ya juye Ruwan zafin Sannan ya maida wani. Koda yayi zafi sai ya juye yayi wanka dashi tare da dauro Alwala Sannan ya dawo ya tashi Nawaz don itama tayi alwalar saboda Biyar har ta wuce.. Salin alin ya jasu jam'i, Saida suka daɗe yana addu'oi Sannan ya juyo yana kallonta da murmushi a fuskarshi yace "good morning sweetheart! Duƙar da Kai Nawaz tayi tare da cewa "ni ya kamata na gaisheki, ina kwana" "Lafiya Lau dear, fatan kin tashi Lafiya, and kuma meye abin laifi don masoyi ya gaida masoyiyarshi? Nan ma dai Nawaz shiru tayi batare da tace komai ba . "Sweetheart Akwai ruwan zafi a Flask kiyi wanka ki shirya inaso mu isa gida da wuri, kuma kinga inaso mu fara zuwa gidan bikin da Inna ta tafi saboda in gaisheta Tare dayi mata godia na gurin fakewa data baki... Murmushi dai Nawaz tayi batace komai ba. "Sweetheart naga Yanzu komai saidai kiyi murmushi, kin dena magana, ko kunyata kike ji? Tashi tayi da sauri tare da shigewa daki batare data kula Shiba, (Mutane zasuyi mamaki saboda nace Aayaan ya hura wutar coal, to amma ba abun mamaki bane saboda soldiers kullum suna daji babu abinda basayi, kumani ina kewaye ne da soldiers iri iri, daga kan navy, army har Air force) A gurguje Nawaz ta shirya Sannan ta fito ta sameshi yana zaune inda yake, yana ganinta ya miƙe tare da cewa "za'a bani one hug? Ko in hakura? Ita dai batace komai ba, kuma bata matsa daga inda takeba, hugging ɗinta yayi na two sec sannan yace "to kwaso mukullin kofar mu rufe mata gidan idan munje sai mu bata.. Har sun shiga Mota Nawaz ta hango hadiya tana tawowa, da sauri tace yaya Aayaann pls ga Wadda tayi Min kunshi can, don Allah ka tsaya muyi Sallama. "You have More Time, lokacina nakine kiyi abinda kike so! Fita tayi daga motar Tare Da yiwa hadiya murmushi "yau zan koma ki bani Number ki, zamu riƙa yin waya. Saroro hadiya tayi, aini baki cemin Yau zaki tafiba, to zuwa gidan bikin fa? Nifa na shiryo ne. "Au to Shikenan ma, shiga muje Kawai daga nan sai muyi Sallama. Baya ta buɗe ta shiga tare da gaishe da Aayaan, ai Saida ta haɗiyi wani tsinkakken miyau ganin Aayaan da tayi "tab hakan mijin nata yake? Lallai Dole tarika gyara, wannan kyau , hu'um. Abinda hadiya take raya wa kenan a zuciyarta. Amsawar da Aayaan yayi ne ya katse mata tunaninta, Ƙara cewa yayi "dama ke kika gyara min amarya ta? To gaskiya kinada babbar kyauta, Nagode Kusan suma hadiya tayi "wai yau itace wannan mashahurin me kuɗin yake godewa, ai ita ta gama jin daɗin duniya.. Haka dai har suka isa gidan bikin, Aayaan be Bari Nawaz ta fita ba saboda maza daya gani cike da Kofar gidan, hadiya ce taje ta kira innan. Ai Koda Inna ta fito tsayawa tayi tana kallon motar dasu Nawaz suke ciki, cewa tayi " Lallai wani jinkirin Alkhairi ne, ai bata ƙara tsinkewa ba Saida sukayi ido huɗu da Aayaan. Tasan photunan Aayaan ɗin a gurin ɗan autanta saboda beda aiki kullum sai cewa Allah yasa ya zama soldier Kamar Aayaan... Ko banza tasan bata gyara Nawaz a Banza ba, sosai suka gaisa a mutunce tare dayi mata godia sosai, ita kuma ina ta noƙe murya "kada kaga sanda tazo bance ta koma ba, abinda yasa bance ta koma ba shine kar inje tayi wani gurin kaga yarinya ce ba Wani hankali suke da Shiba. Murmushi Aayaan yayi Tare Da cewa "Babu Komai Inna mun gode, Yanzu sazu tafi chan Maidugurin ne, idan naje zan hadaki da Mummy na sai ku gaisa. Wrappers ɗin yan ɗari Biyar Guda biyu ya miƙawa hadiya yace taba inna, ita kuma ya bata wrappers ɗin yan ɗari biyu yace nata ne, ai kuwa hadiya sai godiya takeyi, ita kuma inna ta Fara noƙe noƙe "anya ayi haka kuwa? Tafiya dai Aayaan yayi ya barta tanata shi mishi albarka..... Saida suka isa flyover Sannan ya kira securities ɗinshi suka dauki Hanyar komawa gida, tuƙin ya basu sannan suka koma baya shida Nawaz Tun ba'a yi nisa da tafiya ba yaga Nawaz ta fara gyangyadi, Amma ƙarfin hali ya hanata ta kwanta.. Kallonta yayi Tare Da cewa "kirjina yana maraba dake akowane irin lokaci.. Kin kulashi tayi ta kauda kanta gefe Amma tana murmushi ƙasa ƙasa. Misalin ƙarfe ɗaya saura suka tsaya a Gaya sukayi Sallah Sannan sukaci gaba da tafiya.... Anan Barci yayi awon gaba da Nawaz ba Tare data shiryaba, ai tuni ta faɗa jikinshii, shikuma ya rungumeta tsaff. Sai gurin ƙarfe Biyar suka isa gida, hamdala yayi wa Ubangiji Tare Da ciccibar Nawaz yana shiga falourn da ita Bayan yacewa securities ɗinshi su shigo da kayayyakin dake cikin motar harda na Boot. Wata irin ƙara Aseey ta kwala Tare ta nufar Aayaan da gudu tana cewa. "Mummy ki fito yaya Aayaann ya dawo da sister Nawaz!!! A firgice Nawaz ta farka, sai ganinta tayi a hannun Aayaan, gefe kuma ga Aunty Aseey tana murmushi, ita kuma Mummy tsaye take a bakin kitchen ɗin riƙe da ludayin girki itama murmushin takeyi, shikuwa honourable muhsien harya bude kwalin chocolate ya fara ci, sai Wata data gani a zaune a kan kujera ta ɗora Kafa ɗaya kan ɗaya tana aikin taunar chewing gum, ita Nawaz ma sai taga Kamar hararar ta takeyi. Cewa tayi "saukeni" a hankali. Sauketa yayi aikuwa Aseey ta rumgume ta tanata murna, itama Mummy karasowa tayi suka rungumeta juna, babu wanda yayi mata Maganar guduwar da tayi saboda Ashley da take zaune a faloun, basason wani yaji family issues ɗinsu saboda kada su jawa kansu abin Magana... Mamakin abin da Ashley tayi mummy takeyi, "ke Ashley bakiga matar yayanki bane kike zaune baki tashi kin tarbeta ba? Yamutsa fuska Ashley tayi "Mummy aini ban san taba" sai kuma ta kalli Nawaz tace "sannunki" Sam Nawaz neman miyau tayi a bakinta ta rasa saboda Cewa da Mummy tayi ita ɗin matar Aayaan ce! "Ko kallon Ashley bata yiba, sakamakon jin jiri yana Neman kwasarta, sai sannan Mummy ta lura da abinda tayi ganin Nawaz zata zube musu Anan, Aayaan tayiwa magana da ido akan ya ɗauke ta ya Kaita ɗaki.... Aikuwa suna shiga ta fashe da kuka, Mummy ce ta Kalli Aseey tace "Aseey maza kisan yanda zakiyi ku fita keda Ashley, banason taji wani Abu dazai iya jawo mana ɓaraka. Aida sauri Aseey taje ta samu Ashley tace tazo ta rakata ShopRite, Ashley mayyar yawo kuwa ta mike tana washe baki, muhsin kuwa ko kallonsu beyiba yaci gaba da cin chocolate ɗinshi har suka fita daga falourn.. Wani Abu Nawaz takeyi Kamar me aljanu, duk idonta sun kaɗa sunyi ja, sannan sai Wani shure shure takeyi. Addu'a Aayaan ya Fara yi mata Yana tofa mata, ita kuma mummy ta fita don ɗauko ruwan zam'zam. Sosai Aayaann yake yi mata addu'a tare da shafa Mata Ruwan zam'zam ɗin a fuska, wanda Mummy ta tsiyaya a kofi ya amsa ya karanta fatiha ƙafa bakwai Sannan ya barbaɗa garin ganyen magarya a ciki Tare Da Kafa Mata kofin a bakinta, Saida ya tabbatar ya zuba a bakinta sannan ya cire kofin, aukuwa nan ta fara atishawa, sai kuma a hankali ta riƙa ajiyar zuciya... A tare sukace Sannu Nawaz! Buɗe ido tayi ta kallesu sai kuma ta maida ta rufe da sauri, don wani nauyin Mummy taji ya kamata... Har dai da gaske ita matar Aayaan ce yazatayi da wannan Abin Kunyar data tafka? To yaushe ne ma ta zama matar Aayaan ɗin? Fara Maganar da Mummy tayine yasa Nawaz ta tsaida tunanin da takeyi tayi shiru tana saurarenta. Tsaff mummy ta zayyanewa Nawaz komai tundaga sanda sukayi magana da baffa har zuwa randa aka daura aure babu abinda ta ɓoye mata... Mummy batayi shiru iya namba har Saida ta kara da cewa "Nawaz ina sonki da yawa! Yaro Nama yana sonki sosai, kaunar da muke Miki ce tasa muka nemi alfarmar haɗa zuri'a dake, Sannan ƙin sanar dake da akayi dukni naja, saboda nina roƙi hakan saboda a tunanina idan aka faɗa Miki a lokacin zakiga kamar anyi Miki karfa karfa ne, amma ina Neman afuwarki, Don Allah ki yafe min, Kuma ko yanzu kikace bakyason Aayaaaann Wallahi take zansa ya rubuta Miki takarda... Shiru Nawaz tayi tanajin abin kamar almara "wai itace matar Aayaan! Tsugunawa Mummy tayi tare da cewa "Nawaz kiyi magana, kuma wallahi Duk Abinda kikace shi za'ayi. Da sauri Nawaz ta miƙe tare da kama hannun mummy tana mikar da ita "mummy kefa mahaifiya tace a gurina kuma duk Abinda kika umarceni dayi zanyi, Don Allah ki Dena Duka min.. Aayaann yana gefe yana murmushi, sosai Mummy ta rumgume Nawaz, shima Aayaan Sai ya haɗa su ya rungume.. Nawaz kam nauyinshi ne ya saukar mata a kirji kamar an ɗora Mata gungumen ice... Sifsif ta juya ta fita bayan Aayaan ya sakesu, dakin da aka bata ta shiga tare da zama a gefen gado, Azahiri ita bataji farin ciki ba kuma bataji baƙin ciki ba, saidai Wani Abu dayayi mata nauyi a zuciya.. So take ta fadawa Wani ko zata samu sauƙi a zuciyarta, kuma tana mamakin meyasa umminta bata fada mataba! Tunanin kiran Nafisa tayi, sai kuma ta tuna Cewa Nafisa garmaho ce ba lallai ta fahimcetaba.. Cikin aljihun doguwar rigar jikinta tasa hannu ta ciro wayarta, Tabbas Khadija ya kamata ta kira, sosai taji daɗi Kasancewar ta haddace Number KHADIJAT tun tuni, domin zan iya cewa ma batada kawar data fita, sauran duk bogi ne. Number ta loda tayi dialing, aikuwa ƙara Uku ta ɗaga Tare dayin sallama. Nawaz na amsawa khadija tace "nayi fushi dake besty, gaskia baki kyautaminba, nazo gidanku yafi so goma amma bakyanan kuma kinsan bana shiri da umma balle in tambayeta. "Kiyi hakuri deejert, wallahi Yanzu haka ina cikin damuwa, jin rayuwata nakeyi kamar ba tawa ba.. Ƙasa da murya khadija tayi "kawalli meke damunki? Gyaran murya Nawaz tayi Sannan ta Fara ba Khadija labari, tundaga sanda suka haɗu da Sarfraz har zuwa yanzu da Mummy ta gama fada mata cewa Aayaan mijin tane. Kasa magana Khadija tayi sai salati takeyi da sallallami, daga baya kuma tace Lallai umma, abin nata har yakai ta Turo amiki fyade, ke duniya. Amma Nawaz naji daɗi da Allah ya kuɓutar dake daga hannun ƴan ta'addan nan, kuma kika tsira daga gurin wanda yaso yayi Miki fyade. And Ina tayaki murna da Allah ya baki gwarzon miji me kaunarki tsakani da Allah. Naji daɗi sosai da Hakan ta faru kema sai kiyi ta yiwa Allah godia. Dama kullum idan nayi Sallah saina saki a addu'a, saboda duk set ɗinmu kinfi kowa kokari daga islamiyya har boko gakida kyau, to amma sai Allah yayi jinkiri kawo miki miji, Ashe tanadi yakeyi Miki. "Khadijah nifa abinda yake dan tayar Min da hankali shine gani nakeyi Aayaan Kamar ba sona yakeyiba sha'awata yakeyi, saboda bini bini yayi ta taɓa min jiki.. "Kai Nawaz! Wai yaushe zaki Dena wannan shirmen nakine? Kefa yanzufa kika gama faɗamin cewa shi jinin Asia ne, saboda Maman shi Yar Pakistan ce kuma a Sudan ra girma, to kuwa kinga dabi'un mu ba ɗaya bane, su sun maida runguma da sunbata ta zame musu al'ada, hakan da yake yi wallahi kauna ce, domin da wani ne ya samu damar da Aayaan ya samu a kanki da tuni ya buga kwallo cikin raga, amma shi ya tsaya yana ta lallaba ki. Ke in faɗa miki iya damar daya samu jiya a gidan inna ta isa yayi abinda zaiyi ya gama. To amma saboda kaunarki da yake yi ita ta hanashi bawai don kinfi karfin Shiba. "To khadija ya zanyi da sarfraz? "Hmm Nawaz kenan, bazanyi mamaki ba tunda ke Yar farice, me zakiyi da ɗan karamin yaro, so kikeyi ki aureshi nan gaba kuma yace kinyi mishi tsufa? To ki kwatanta ni babu ruwana, da kike zancen sarfraz yanzu, zakisa Aayaan ɗin ya sake kine? Abinda nakeso ki lura dashi shine Sarfraz harda kuruciya, kuma shi kyau kawai kikeyi masa bawai Wani abuba, kuma Yanzu abinda zakifi focusing akai shine idan yana raye Allah ya bayyana shi, Ni kaina naji tausayinshi sosai domin jarumi ne kuma ya taimake ki matuka, Allah ya bayyana shi.. "Ameen Nawaz tace tare da cewa Nagode sosai khadija zanyi tunani akai, Yanzu sai munyi waya, sallama sukayi Sannan ta kashe wayar tana juya maganar khadija a zuciyarta... Ji tayi an turo ƙofa, tana Daga kai taga Aayaan ne tsaye har yayi wanka ya shirya.. Kusa da ita ya karaso ya tsuguna tare da kama hannuwanta, "sweet heart pls kiyi min addu'a zanje wani aiki but In'sha Allah bazan wuce 3weeks ba zan dawo. Mamaki ne sosai ya kama Aayaan jin da yayi nawaz tace "Allah ya tsare, kuma Allah ya dawo dakai lafiya cikin aminci. Mikewa yayi Tare Da rungume yana jin wani farin ciki da be taɓa jin irinshiba... Sunbatar ta yayi sannan ya fita daga Dakin yana haɗa hannun wuri ɗaya alamar love🫶🫶🫶🫶. Yana fita kafin ya shiga Mota kiran haidar ya shigo wayarshi sakamakon ya kunna wayoyin bayan sun dawo, dama abinda yasa ya kashe wayar saboda wannan lokacin ya wareshine ga Nawaz.. Yana ɗagawa haidar yahau faɗa yana cewa " wai me yasa ka kashe wayane tun jiya, sai kiranka nakeyi taƙi shiga. "Meyafaru basai kaji me nakeyi ba ai! Sarfraz ya farfaɗo, kuma anytime daga Yanzu zai iya tashi. Ai Saida ayann yayi wata kabbara, sannan yace haidar ganinan, yanzu zan zo In'sha Allah, dama zamuje Eritrea ne nida Colonel amma yanzu zan nemi alfarmar kwana ɗaya saboda nazo na ganshi, komai dare ka jirani haidar i am on my way... Kiran colonel yayi akan cewa su su tafi zuwa gobe zai riskesu achan Eritrea ɗin. Allah ya taimake shi koda yaje airport akwai night flight Kuma saura Mutum biyu, ba'a ɗauki lokaciba jirgin ya tashi.. Misali karfe takwas da rabi jirginsu Aayaann ya sauka a England, Kiran haidar yayi yazo ya daukeshi, suna isa asibitin suka tarar sarfraz ya tashi yanata daru wai ina Nawaz da mummyn shi da Daddy... Hassu kam tana gefe Kamar wata yar tsakuwa, ganin bema nuna yasanta ba. Aayaann ne ya ƙarasa ya riƙe shi tare da kwantar mishi da hankali, sosai sarfraz ya nutsu yana sauraron shi... "Ina Nawaz" abinda SARFRAZ taketa mai mai tawa kenan. "Tana gida, tana gaisheka ma". "Babu abinda ya sameta Koh? "Eh babu" cewar Aayaan tare da rike sarfraz yana mikar dashi don su tafi zuwa gidan haidar. Koda suna hanya babu abinda sarfraz yakeyi sai raba idanu, da dai yaga abin yafi karfinshi sai cewa yayi, wai nan inane? Bandi ne tace "England ne? Wani ihu SARFRAZ ya saki tare da cewa wai dagaske nine a England? My best country.... Aayaann kam sai murmushi yakeyi ganin SARFRAZ cikin farin ciki. Koda aka isa gidan haidar namna dai hassu tsumu tayi tana kallon shi, Kallonta SARFRAZ yayi yace "wancan me kama da alia bhat dinfa wacece? Haidar ne yace mamar kace, saboda sanda bakada lafiya ita takeyi maka komai, Kama daga wanka, wanke poo dadai sauransu..... Zaro ido sarfraz yayi "haba don Allah Nidai ku dena irin wannan abin kada ta rainani.... Haidar bece komai ba face wayarshi daya ciro a aljihu yana danne danne sannan ya miƙawa sarfraz ɗin, Zaro ido SARFRAZ yayi yana kallon video ɗin, shine daga shi sai gajeren wando yana rikici wai shi hassu ce zata yi mai wanka ga haidar a gefe yana Cewa kabari inyi maka, amma sam yace shi na Hassu yakeso.. Wani miyau ya haɗiye "yanzu wannan yarinyar tasan komai game da shi kenan? Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, duk sai yaji kunya ta kamashi.. Wayancewa yayi yace to saime ma, ai ƙawata ce, ko alia bhat? Murmushi tayi tare da daga kai... Haka dai aka kwana yin raha, Aayaan ya faɗa mishi cewa shi yayan shine amma sauran karin bayanin saisun koma gida. Koda safiya tayi da Aayaan Zai tafi Eritrea sai yaba sarfraz daya daga cikin ATM 🏧 CARD Dinshi, akan duk abinda yake bukata ya siya. Ai kuwa Aayaan yana tafiya bayan haidarr ya tafi asibiti SARFRAZ ya dauki motar haidar, ba Tare dayasan ko inaba yace su Hassu da bandi su hau, map ya saita saboda kada su kasa dawowa.. Kasancewar titunan waje básuda cinkosi yasa SARFRAZ ya riƙa falfala gudu, wani guri da ake Saida waya ya tsaya ya siya aka haɗa mishi komai, dama shifa, sunan daya gani a jikin Kayan Aayaan yakeso ya duba Google yaga matsayinshi... Ai kuwa yana gama dubawa yace hooooniii ashe babban soja ne, wallahi zanyi bura uba ashe.. Tun daga ranar SARFRAZ ya ishi kowa, daga yaje bishiyar kofar gidan wancan ya ciri guava, sai yaje waccan ya ciri lemun, kuma haka duka zai bata maka kofar gida da ganye, in kayi magana yace shi ƙanin Captain Aayaan ne.. Gaba ɗaya ya ishi haidar, kuma ga gudun bala'i a titi idan ya ɗauki mota.. Yauma zuwa yayi ya siyo (racer) keken nan irin ta yan tsere . Hawa yayi ya zauna sannan yace bandi ya hau baya, ganin hassu na tsaye tana kallonsu yasa sarfraz yace kema zakije? Ɗaga kai tayi alamar eh. Aukuwa yace zo kihau gaba, amma ki rungumeni saboda Kada ki fadi.. jan keken yayi da gudu yahau titi, aikuwa mutane sai kallonsu sukeyi Kasancewar a dokar ƙasar ko Mutum biyu ba'a yarda su hau keke ba balle uku, sai kuma gashi su uku sun hau.... Saiya miƙa hanya da gudu saiya cire hannunshi akan keken yana dariya. Sosai mutane suka taru suna kallonshi Inda acikin masu kallon aka samu wani ya kira Yan sanda... *MATAR RASHEED* ✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *53* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji ✍️* Sam SARFRAZ beji zuwan ƴan sandan ba sai ganinsu yayi a gabanshi, ai kuwa duka suka sauka a motar tare da zagayeshi. Daya daga cikin su ne ya kama hannun sarfraz ɗin tare dasa mishi handcuffs, tasa ƙeyarshi akayi har cikin mota sannan aka tasa su bandi da Hassu, sosai SARFRAZ yake roƙonsu akan su bari ya kira yayanshi, amma fir Yan sandan suka ki yarda. Haka SARFRAZ yanaji yana gani aka tafi dasu, wasu daga cikin turawan kuwa sunata dariya, dama akwai waɗan da Sarfraz ɗin ya addaba a cikinsu. Haidar ne shima tafe akan titin domin komawa gida saboda yau beda shifting ɗin rana, har ya gifta motar Yan sandan sai kuma yayi reverse ya juyo saboda wasu ya gani aciki kamar su Hassu... Da gudu yabi motar, ai kuwa su ya hango a ciki, tsaki yayi "wallahi idan Aayaan bezo ya maida yaron nan gidaba wallahi nasan tsaff zaisa nima a koreni a ƙasar nan, ko yanzu me yaje ya aikata Oho.. Ƙarawa motar gudu yayi tare da shan gaban Yan sandan, parking driver ƴan sandan yayi tare da dirowa daga cikin motar yana jaraba..... Ganin haidar da yayi sai ya dena fadan ya fara tambayar shi meyasa ya tsare musu hanya? Saboda yasan haidar ɗin, kasancewarshi babban likitane a fannin abinda ya shafi ƙwaƙwalwa. Hakuri ya fara bashi tare da cewa laifinshine daya manta be rufe SARFRAZ a cikin gida ba. "Kamar ya laifinka? Bayan mu mun kama shine da laifin karya mana dokar hanya! "Eh yallabai, abinda yasa nace maka haka shi ɗin majinyaci nane, kuma yanada matsalar kwakwalwa ba'a saiti yakeba sha tara sha tara ne. Girgiza kai ɗan sandan yayi Sannan yace tabbas da alama, don Nasan me hankali bazaiyi wannan abin da yayi ba, amma don Allah ka riƙa kula dashi sosai kada wata rana yaje yayi abinda zai Cutar da kanshi.. Sosai haidar yayi mishi godia tare da cewa in'sha Allah zai kula dashi dakyau. Sakinsu akayi aka cirewa SARFRAZ handcuffs ɗin sannan aka fito Musu da kenen su, su kuma Police ɗin suka tuƙa motar su sukayi gaba. Suna tafiya haidar ya fara yiwa SARFRAZ faɗa "kai bakajin Magana Koh? Nayi maka nasiha nayi nayi amma kaƙi ɗauka, wai ya kakeso nayine? So kake a koreni daga garin ko? Yanzu in banda abinka ya za'ayi mutum uku suhau keke guda ɗaya, ko tsoron lafiyarku bakwa yi ko? Shidai SARFRAZ tunda haidar ya Fara fada ya duƙar da Kai yayi shiru kamar faɗan yana ratsashi. Hassu haidar ya kalla Sannan yace "kema kina matsayin mace amma kina biye musu Koh? Kici gaba idan wata Rana suka karyaki ke kika sani.. Keken ya gungura ya sakata a Mota sannan yace musu " ku Wuce ku shiga mota mu koma gida. Sif sif suka shige seat ɗin baya suka zauna suna raba idanuwa. Koda suka isa gida a waje sukaga Madam haidar itama ta fito zata shiga Mota. Da sauri ta ƙarasa gunsu tare da cewa "sweetheart Ashe ka amso su? Wallahi yanzu Florence yazo yake cemin wai Yan sanda sun kama baƙi na sun tafi dasu. Bakaji zuciya taba, Yanzu haka na shirya ne zan tafi station ɗin. Cewa yayi "Wallahi basa ji sam, ace kullum daga wannan sai wancan Nidai na gaji Gaskiya, Aayaan Zan kira wallahi yasan yanda zaiyi su koma gida Kafin susa a koremu gaba ɗaya, yanzu haka da kika ganni dasu karya na shararawa cp ɗin shiyasa har ya bani su cikin Salama, amma da Wallahi sai munsha wuya zai bamu su. Su sarfraz suna gefe Duk sunyi tsulu tsulu kamar tsintsaye sai raba idanu sukeyi. Gida suka shiga duka, kowa yayi nashi gefen, haidar da Madam sukayi sama, bandi da sarfraz kuma sukayi dakin da aka basu a Matsayin nasu, itama hassu tayi nata. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Nawaz kam tun daga ranar data san ita matar Aayaan ce ta fara wasan ɓuya da mummy, koda wasa bata bari su haɗu sai dai bisa kuskure, shima suna haɗuwa zata gudu, ita kuma Mummy Sai dai tayi murmushi ta wuce, kuma kunyar Nawaz sosai take birgeta, fatan ta ɗaya wata rana su saba sosai. Aseey kuma tuni ta maida Nawaz kakarta Domin kullum cikin tsokana take, daga tace matar ƙanina kishiryawa amarci don yana dawowa da sai an wuce gurin, sai kuma tace wannan kibar da kikayi ƙanina zai kwashi garaa. Ashley kam ta tsani Nawaz kamar ta buɗe ido taga Babu ita, gani takeyi kamar ta kwashe komai, saboda tafita kyau nesa ba kusa ba, gashi ta lura su mummy suna matuƙar kaunarta sosai sosai, komai suce Nawaz. Abinda yafi ƙonawa Ashley rai shine yadda kullum Aseey zata zauna tana bata labarin irin ƙaunar da Aayaan yakeyiwa Nawaz. Ita kuma Nawaz ko a kwalar ta domin bata samma tana yiba, ita abinda ke gaban tama ya isheta. Mummy ce zaune Ita da Aseey suna hirar wadda za'a kira tayiwa Nawaz gyaran jiki kafin su tare, dukda sun lura Nawaz ɗin ta chanza ba kamar daba. Aseey ce tace "Mummy kawai ki kira Aunty Koutume kawai tazo tayi mata, kinga lokacin bikina datayimin Saida kowa yace nayi kyau sosai. To in banda abinki Aseey kinsan Koutume tana Sudan kuma ba Lallai tazoba, tunda a chamma kullum a tsaye take bata zama saboda aiki. Cewar Mummy tana kallon Aseey don jin wace amsa zata bata. "Haba mummy! Ƙawar kice fa, kuma nasan idan kikayi mata magana zatazo, kinga daganan nima sai tayimin kafin in koma England. Harara Mummy ta balla mata "au kice kanki kike yiwa campaign dama" "A'a wallahi ko nata ma aka samu Ni ya wadatar dani sosai. Haka suka ajiye akan Mummy zata kirata taji ko zata samu damar zuwa. Ita kuma Aseey ta miƙe Tare Da fita tana rawa, dakin Nawaz ta shiga tana cewa "lovely sis Ina kike ne? Fito kiji abin Alkhairi! Nawaz dai daga kai kawai tayi ta kalleta ba tare data ce mata komai ba domin tasan bazai wuce zancen Aayaan zatayi mata ba. Kusa da ita ta zauna sosai ta naniƙe mata kamar zata shige mata jiki "sister yanzu muka gama Magana da Mummy akan za'a kiramiki mai gyaran jiki daga Sudan wadda zata maidake ki koma balarabiya duk da kema ba baya ba, lokacin da tayimin na biki wallahi nima kaina saida na koma sha'awar kaina, hmmm dama ace baya na dawowa..... Itadai Nawaz kallonta takeyi batare datace komai ba, saida ta gama maganar sannan tace "Ni dai abar wani gyaran jiki Gaskiya, wallahi batun Auren nan sai nake gani Kamar mafarki wallahi. Kama baki Aseey tayi 🤔 "Eh Lallai tunda ya barki kisha iska ba, da ace aikin gama ya gama Aida kin tabbatar Auren gareki, ƙilama Yanzu da ciki gareki! Rufe fuska Nawaz tayi "Gaskiya Aunty Aseey kidena min irin wannan maganar kunya kike bani wallahi. "Hmmm Nidai na faɗa miki, kima shirya kafin ya dawo wallahi don bazan yarda da wannan zaman banza da kukeyiba. Gaba daya kunyace Ta rufe Nawaz, tama rasa yanda zatayi, itako Aseey ko a jikinta kuma ita har zuciyarta da gaske takeyi. Koda Aseey ta fita Nawaz kasa fita faloun tayi, sai kawai ta janyo wayarta ta kunna don ta kira umminta, saboda tun Ranar da suka gama waya da khadija ta kashe wayar. Tana kunna wa message"s suka riƙa shigowa, kuma duk Aayaan ne ya Turo mata, Harda su voice messages. A hankali ta riƙa bi tana buɗewa tana karantawa, sai murmushi take yi, domin duka sakonnin ƙorafine akan ta taimaka ta buɗe wayarta domin yanason yaji muryarta, inba hakaba zuciyarshi zatayi bindiga. Tunani ta fara yi akan ta kirashine ko Kada ta kirashi, chan dai Wata zuciyar tace ki kirashi mana, ko Babu komai ai ka gaida me gaisheka.. Dialling ɗin number tayi sai kuma taji Kamar ta yanke domin ji tayi zuciyarta ta Fara bugawa da ƙarfi da ƙarfi. Bata ankara ba sai jin Muryar Aayaan tayi yana cewa "sweet heart kin wahalar Dani Wallahi, kin sani a damuwa, na rasa mekeyimin daɗi a Duniya. Ko Babu komai ai ya kamata ki kunna wayar ki koda ke bazaki kiraniba Ni zan kira, amma saiki shareni kamar baki damu daniba, ko Bakya sona ne? Duk kunya ta kama Nawaz, kasa cewa komai tayi sai dai murmushi da takeyi ƙasa ƙasa... "Bakice komai ba Sweet love, ko Bakya sona ne? "Um-um kayi hakuri bazan kuma kashewa ba... Wani dadine ya ziyarci zuciyar Aayaann Domin ya fara Ganin alamun Nasara "kada ki bani hakuri Domin kece zuciyata kuma bazan taɓa yin fushi dakeba har abada. Yanzu dai jibi zan dawo don wallahi na kasa tabuka Komai achan ɗin, kinsan fa kinbi jini da duka jijiyoyin jikina kin zuba musu gubar sonki, bana iyayin second ɗaya ban tuna dake ba. Amma Ni nasan ba'a sona Kawai dai ana yimin kawaicine, koba hakaba? Shiru Nawaz tayi kamar Wadda Ruwa ya cinye, ita dai wallahi su Aayaann da Aseey suna bata mamaki, Sam basa ɓoye abinda ke Cikin zuciyar su, Sannan basajin Kunyar faɗar Komai.. Aayaann ne ya Kuma cewa "sweetheart bakice komai ba! PLS Nidai Ina roko a taimaka a ajiye Kunyar Nan gefe guda, domin nifa Babu Wata kunya a tsarina Don Cutar dani zatayi saboda nine ke kuma kece Ni, To meye wata kunya zata shigo ciki. Namma dai Nawaz shiru tayi ta kasa cewa komai. " Shikenan sweetheart tunda tsanar da kika yi min takai haka babu komai, Ni nasan matsayina yanzu. Da sauri Nawaz tace " wallahi ya Aayaan ban tsanekaba kawai dai kunya kake bani. Murmushi yayi "da naso na Daga miki kafa amma naga Kunyar nan taki zata hanani rawar gaban hantsi Dole nayi saurin kawar da ita. Kila na samu Nima a fara kula dani kamar Yadda ake kula da sauran magidanta. NAWAZ kam ji tayi kamar ta nutse a gurin tsabar kunya, duk ta daburcewa gaba ɗaya. "Yanzuma kin kuma yin shirun ne? Shikenan babu komai Kawai yanzu ki shirya wa dawowata Don a randa na dawo zanyi fatali da wannan Kunyar da take wahalar Dani, Kinga kila ma a Samar Wa Mummy jikoki Yan biyu masu kama dake. Da sauri Nawaz ta yanke wayar tare da dafe ƙirji domin gani takeyi ma kamar yana gabanta... Shikam Aayaan yana can yana dariya, don dama yana sane yace Bari ya tsokaneta yaga ya zatayi. Tana wannan halin saiga Aseey ta shigo niƙi niƙi janye da akwati har guda biyu, saida tazo gaban Nawaz ta ajiye su tare da cewa "Ni nama manta sai yanzu na tuna, tun randa Aayaan zai tafi yace na Kawo miki tsarabar ki daki. Akwatin Farko ta nuna "kinga wannan tsarabar kice tun wadda ya siyo miki sanda yaje Abuja, shikuma wannan dayan akwatin tsarabar da yayi miki sanda zai je ya tawo dake daga Zariya ne.. Kuɗaɗen hannunta ta miƙa Mata, wadannan kuma kudin daya bakine randa kika gudu, su kuma wannan cewa yayi na baki ranar dazai tafi Eritrea manta wa nayi, kiyi hakuri.. Sakin baki Nawaz tayi ta tsaya tana kallonta, duk wannan tulin kayan ne za'a ce nata ne, sannan ga Wasu kudi har wrappers huɗu wai suma nata ne, to ina zata kaisu?.. "Ni gaskiya Aunty Kayan Nan sunyi mini yawa, Bansan ya zanyi dasuba, kuma kuɗin ki kike nabar miki. Harara Aseey ta zabga Mata. "wato Ni zakiba kyautar kuɗi koh? To sannu da ƙoƙari, ida konasu zakiyi saidai kiyi amma banso. Tashi tayi ta fice daga ɗakin ba Tare data ko saurari me Nawaz ɗin zata ƙara cewa ba. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Wani ba gani kamar SARFRAZ ya dire ta window, yana dirawa saiga bandi shima ya diro, ikon Allah!🤔 Hassu ce naga itama ta diro, charaf sarfraz ya rike ta saboda kada ta faɗi. Sif sif suka wuce harabar gidan, mukulli ya ciro daga aljihunshi ya buɗe motar haidar suka shige ciki, ai kuwa ya figeta da gudu suka shiga cikin gari. "Bandi zaka gane wadannan Yan iskan turawan da sukayi mana dariya ɗazu sanda Yan sandan nan suka kamamu? "Eh zan iya gane wasu amma ba dukansu ba.. bandi Yace tare dayin murmushi "Kada ka damu idan muka kama wasu nasan zasu fito da sauran ne.. Sosai ya miƙa titin da gudu, duk wanda ya hango shi sai dai ya kauce da gudu. Suna Isa anguwar yaja wani wawan burki saida hankalin kowa ya dawo kansu... Barkanmu da juma'a, yau Babu yawa amin afuwa. *MATAR RASHEED✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *54* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Parking ɗin motar yayi ya fito waje, suma su hassu da bandi suka fito, itadai Hassu Tunda taji cewa SARFRAZ yazone ya Nemi wata fitinar taji zuciyarta nata bugawa... Kusa dashi ta matsa Sannan tace "sarfraz don Allah ka rabu dasu, tunda har Allah yasa ba'a rigada an kaimu chaji office dinba ka kyalesu. Kuma ko yanzu da suka ganmu nasan dole suyi mamakin ya akayi aka sakemu. "Eh wallahi, Nima a nawa Gara ka kyalesu kawai" cewar Bandi yana dafa kafaɗar SARFRAZ. Shiru SARFRAZ yayi na ƴan daƙiƙu Sannan yace "to Shikenan tunda kunce haka zan rabu dasu, amma wallahi idan wani shashasha ya kuma kallonmu yayi mana dariya wallahi saina fasa mishi hanci. Cikin motar suka shiga amma bada nufin komawa gidaba sai don su shiga gari su yawata. Cikin rashin Sa'a sunzo wucewa ta gefen wani Filin kwallo aikuwa aka samu wani yayi dagon shot sai a kan Hassu, ji kake "Tummm" dayake motar irin me budadden saman nance... Baya hassu tayi kamar wuyanta ya karye tare da sakin wani irin marayan kuka "wayyo yaya bandi wuyana ya karye, zan mutu.... Wani irin wawan burki SARFRAZ ya taka, cikin hanzarin dabesan yanada shiba ya dira daga gidan gaba tare da zuwa gefen inda hassu take yana Cewa ɗaga kanki mugani, ya kan yakeyi Miki? Zaki iya magana? Ganin Irin hawayen da yake zuba a idon hassu yasa yasan Cewa ba ƙaramar azaba takejiba. Juyawa yayi ya nufi cikin filin kwallon tare da ƙarewa waɗanda suke dariya kallo, da sauri Bandi yace "SARFRAZ ka shigo kawai mu tafi gida, kada kace zakayi musu wani abu, nasan bada gangan suka buga mataba. Ko takanshi SARFRAZ bebiba yayi cikinsu da hanzarin shi, yaron farko ya damƙarwa gashi ya fara wujijjigashi iya ƙarfin shi, Sannan ya fara naushinshi a baki da hanci "ance muku ita ɗin banza ce? Ko ance muku ita din batada galihune? Wato so kukeyi ku kasheta ko? Dama ai ɗazu harda Kai akeyimana dariya... Memakon sauran su kawo mishi agaji sai kowa yayi ta kanshi, cikin ƙanƙanin Lokaci duk suka watse a filin, da sauri bandi ya fita daga motar yaje Yana riƙe SARFRAZ tare da cewa "sarfraz ka sakeshi kada ka kashe shi, bafa a kasar mu muke ba, don Allah ka bari mana! Da kyar dai bandi ya iya amshe yaron a hannun SARFRAZ, shikuma yaron yanajin SARFRAZ ya sakeshi ya arta a guje, dayake gurin Kamar park yake babu wasu mutane sosai a gurin..... Haba SARFRAZ! Dama haka kakeda baƙar zuciya, to daka kamashi kana mishi wannan mugun dukan ce maka akayi ta mutu, ko kuma ce maka akayi zata mutu? Ni a ganina da wannan dukan daka tsaya yi gara mu kaita asibiti. "Lallai bandi to bari kaji, idan kai baka dauketa da muhimmanci ba nina dauketa, kana kallon sanda banida lafiya ita ta zamemin kamar uwa, duk wani shirme da wahala ta ta ɗaukar wa kanta kuma ba tare data San koni waye ba! Don Haka Nima na bata Babban matsayi a zuciya ta Sannan babu yanda za'a yi inga wani yayi mata wani abu inyi shiru in zuba ido" duk wannan sharhin da Sarfraz yakeyi a zafafe yakeyi kamar zai mazge bandin. Shikam bandi tsaye yayi baki buɗe yana kallon SARFRAZ har ya gama jawabinsa ya wuce shi ya shiga Mota. "Zakazo mu kaita asibitin ne ko kuwa in tafi? Gaba ɗaya bandi ya tsorata da sarfraz, hakan yasa bece komai ba kawai ya shiga motar ya zauna... Itakam hassu sai wash kawai takeyi ga wuyan harya kumbura kuma yayi jaa.. Asibitin su haidar sukaje, inda aka yiwa SARFRAZ aiki, don haka suna zuwa aka ganesu, basu wani sha wahala ba suka samu docton da zai duba Hassu. Bayan ya gama duk abinda zaiyi ne, yace kwallon ta bigeta sosai ne shiyasa har jini ya mutu a gurin, dayake ya tambaye su Meye musabbabin ciwon. Magunguna ya rubuta yace suje pharmacy su siya Sannan idan suka tashi gobe basuga improvement ba su dawo. SARFRAZ sai Wani lailayeta yakeyi, idan akazo step ma ɗaukar ta yakeyi, shikam bandi bawan Allah sai dai ya bisu da ido yana binsu kamar jela. Nidai matar Rasheed cewa nayi:- *MUJE ZUWA DAI* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Zaune take bayan ta gama duba kayayyakin da Aseey ta kawo mata, mamaki takeyi "waɗannan kayan aiko lefe akayi dasu a wannan ƙarnin sunyi yawa balle ace wai tsaraba... Itafa lamarin Aayaan ya fara bata tsoro.. Ƙarar turo ƙofar da akayi ne yasa Nawaz ta juya da sauri don ganin ko waye ya shigo, Ashley ce tsaye tana ƙarewa ɗakin kallo Tare Da taɓe laɓɓanta Masu kama da ragadada Sannan tace "waike waɗan nan akwatinan danaga ana ta binki dasu wai iya sune lefen naki? Da Nawaz taso ta shareta amma sai taga abin Kamar ya koma rainin wayau, saboda ya za'a yi ta biyota har inuwarda take tace zata faɗa mata magana! Nawaz tanada hakuri saidai ta tsani cin mutunci a rayuwarta. Murmushi tayi tace "tsarabar da Captain ya siyo min ne a hanya sanda zamu dawo! Cikin harzuka Ashley tace "mtsewwwss aikin banza aikin wofi! Wai ke ance miki Bansan asiri kikayiwa Aayaan ba har kika samu yayo ciki dake? Murmushi Nawaz tayi cikin kwanciyar hankali tace "Allah sarki Ashe malamina yafi naki iya aiki tunda har aikinshi yasa Aayaan ya tsallake ki ya shiga duniya cikin miliyoyi ya laluboni, aiko ya kamata naje na ƙara mishi kudi. Cikin hargagi Ashley tace "Wallahi! Allah ya fiki kuma in'sha Allah sai asirinki ya tonu Ni dama nasan ba haka kawai Aayaan yake wannan rawar ƙafar akankiba, Aayaan ɗin da ko kallon Mata bayayi ta ina har zai hango ki? Ai dama nasan sai an haɗa da tsubbu.. Gefe Nawaz tayi da kanta Sannan tace "Meye duka na wani tada jijiyoyin wuya? Naga gurin boka naje, to me zai hana kema kije ki gwada taki sa'ar? Kika sanima kila idan kikayi naki tsubbun shi Aayaan din yace be taɓa ganina ba! Ko be taɓa jin irin sunana ba" Duk wannan maganar da Nawaz ta yaɓawa Ashley cikin ruwan sanyi ta faɗa mata babu hargagi balle daga murya. Itako Ashley tuni ta koma kamar wata zararriya "To wallahi tunda haka kikace to kuwa mu zuba mu gani, za'a ga wanda zaiyi zarrah! Shegiya munafuka. 😊Murmushi Nawaz tayi Sannan tace "to Allah ya bada Sa'a, fatan alkhairi 🙏, kuma shi munafunci nonon uwane nasan kema kinsha, kuma ai dama shege sai shegiya Fuu Ashley ya buɗe kofa tayi waje tare da bugo kofar da ƙarfi, ji kaje "baammmm" Ƙwafa Nawaz tayi tace "kajimin aikin banza, Ni zata nunawa cewa ita shashasha ce? Ko ce mata akayi Ni nasan wani Aayann ne?, in banda hauka ma irin Tata auren ma da ake magana akan shi Nima yaushe nasan dashi? Tsaki tayi ta tashi zuwa bathroom donyin alwala. *KAI ASEEY SAI DAI A BARKI, WATO KE KOMAI SAI KINJI* Tun sanda Ashley ta shiga ɗakin Nawaz ashe Aseey na bakin kofa tana kallonta, labewa tayi a jikin kofa donjin me yakaita shiga ɗakin Nawaz, tunda tasan ko magana ma basu taba yiba. Ile kuwa duk maganganun da sukayi tanaji, daɗi Kamar ya kashe ta jin amsoshin da Nawaz taba Ashley. Ko Banza yanzu tasan ba kowa Nawaz zata bari yaci mata fuska ba. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Aayaan kam ya ƙagu daya koma gurin Nawaz ɗinshi, Sannan gaba ɗaya duk wanda yasan shi yasan ya chanza, saboda duk fadan nan babu Sannan yana zaune shi kaɗai yayi ta murmushi.. Allah yasa ma aikin nasu ba wani me wahala bane, dama ana zargin Yan leƙen asiri sun shigo ƙasar ne shine akace Suzo suyi sumame, idan gaskene su gurfanar dasu a babbar kotun duniya. Tsaff ya gama haɗa kayan shi da iya gejinsu back pack ɗinshi, sosai yake murmushi Domin so yakeyi direct Yanzu ya sauka a London Idan ya kwana gobe sai su ɗauki hanya zuwa gida Nigeria. Sallama yayi da sauran colliques ɗinshi Sannan ya nufi masaukin colonel, sara mishi yayi Sannan ya ƙame, Murmushi colonel yayi "Aayaan dole Akwai abinda kake ɓoye min, Ni nasan ba hakanan kawai ka chanza ba, ko ka Fara Soyayya ne? Zaro ido Aayaan yayi " sir nina isa? "Aayann kenan, duk wanda ya ganka Yanzu yasan akwai abinda yake special a gurinka, kuma shi namiji babu abinda ke saurin chanza shi kamar mace, ko dai daughter Nawaz Taci nasarar sace zuciyar namijin zakina ne? Sosa ƙeya Aayaan yayi tare dayin murmushi donya gane colonel kallonshi kawai yakeyi, tunda dama ance duk wanda ya rigaka kwana dole Ya rigaka tashi. Maganganun da zasuyi sukayi, inda Colonel yace ya ƙara mishi hutun wata biyu akan sauran wata dayan daya rage mishi tunda a banza suka ƙare be samu ya hutaba.. Jin haka da Aayaan yayi kamar ya ciccibi colonel yayi ta rawa da shi, sosai yayi mishi godiya daga bisani colonel Yacewa pilot ɗin private jet dinsu ya kai Aayaan London ɗin... Namma sosai Aayaan yaji daɗi, sallama sukayi Aayaan ya Wuce gurin jirgin suka daga zuwa kasar England. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Parking ɗin motar SARFRAZ yayi a inda suka dauketa, sannan ya ciccibi Hassu a hannu har zuwa bakin window ɗin da suka diro sanda zasu fita, mikawa bandi ita yayi "Bandi riketa, idan na kama nahaura zan leƙo saika miƙo min ita. Amsarta bandi yayi sannan sarfraz ya haura ya dira, sai Wajen cicciba hassu ɗinne aka samu matsala domin bandi be kai sarfraz karfi ba, saida kyar da sudin ludayi ya iya cicciba ta sanna SARFRAZ ya janye ta sai shima bandi ya haura, suna isa falour suka fara sanɗa, aikuwa ganin babu kowa yasa kowa ya arta dakinshi da gudu. Sosai Hassu take dariya, ita wannan kwallon da aka buga mata daɗi taji tunda har tagane SARFRAZ ya dauketa da muhimmanci, kuma ya nuna zai iya yin komai akanta. Shima sarfraz yaji daɗi sosai ganin har suka fita suka dawo haidar be sani ba tunda shi ya ajiye cewa haidar ɗin ya cika s ido ne. Ai su SARFRAZ basuyi minti goma da shiga gidanba aka fara buga gidan da Wani irin mugun ƙarfi kamar za'a jijjige kofar a ajiyeta gefe guda. Jin hakan da sukayi sai kowa yaja bargo Tare Da rufe ido harda munshari irin su sun daɗe dayin barci. Haidar bawan Allah, kwance yake shida Madam Dinshi yana barcin huce gajiya Kasancewar duty ɗin dare yayi jiya, a firgice ya tashi jin irin bugun kofar da akeyi. Sa sauri ta ɗauki riga ya ɗora a saman singlet Dinshi Tare da Cewa madam Dinshi ta tsaya ya dawo tunda takamaimai besan dalilin bugun kofar ba. Koda ya dauki mukullin kofar gidan be fita ba Saida ya leka dakunansu SARFRAZ don ya tabbatar basu suka sashi a wata matsalar ba. Ai kuwa tarar dasu yayi duka suna barci, sosai yaji daɗi don yasan wani abun ne daban ba matsalar su SARFRAZ bace. Yana buɗe ƙofar ya tarar da Wani ɗan saurayi tsaye gaba daya bakinshi da hancinshi sun kumbura sunyi sumtum, dayake farar fata ne duk sun haɗe sunyi jajir. Gefen shi kuma wani Babban mutum ne tsaye shima, amma ga dukkan alamu babban yaron ne, sai kuma kauya tsaye a gefe rungume da file. Haidar ka Banu tunda Aayaan ya aɗaka da Sarfraz, don ma Allah yasa yana hanya. Koya zaku ƙare dasu oho. *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *55* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Gaishesu haidar yayi cikin sakin fuska don a tunanin shi patient aka kawo mishi, Kicin kicin da rai baban yaron yayi tare da cewa "niba gaisuwa ta kawoniba, gurin baƙinka nazo. Cike da mamaki haidar yace "me baƙi na zasuyi maka? "Nazo ne su faɗa min abinda yasa suka kamamin ɗana sukayi mishi wannan ɗanyen dukan Kamar sun kama ɓarawo. Murtuke fuska haidar yayi don yaga alamun rainin wayau a lamarin, shidai yasan sarfraz be taɓa dukan waniba, a dai abarshi da tsokanar fada da shiga sharo babu shanu, idan kuma tayi ƙamari shine ya haurawa Mutane cikin garden yayi barnar fruit Yadda yaga dama. A yaushe su baƙin nawa sukayi mishi wannan dukan? Haidar ya tambaya don tabbatar da zargin su da yake yi nason shiryawa SARFRAZ sharri. "Ko cikakkiyar minti talatin ba'a yiba, don yana zuwa gida ya faɗa min mukayo nan. Wata dariyar rainin hankali haidar yayi "sannu da ƙokari, to ku sani ƙaryarku bata samu shiga ba Saboda Ni Na dawo dasu cikin gidan nan da hannuna kuma tunda suka shiga ɗakunan su basu fitoba domin Yanzu haka barci ma sukeyi, kuma koda ma ba barcin sukeyiba babu Yadda za'ayi su fita waje saboda na rufe ƙofa da mukulli.. Cikin Muryar kuka yaron yace "Wallahi shi ya bigeni. Shidai haidar cewa yayi "na gama magana, domin Babu Yadda za'ayi yara basuyi abuba ace sunyi, dayaga Kamar basu yarda ba sai ya shiga ciki ya taso SARFRAZ ya tawo dashi. Koda SARFRAZ yagansu saida zuciyarshi ta buga, amma dayake cikakken ɗan basaja ne sai ya maze beko nuna alamar rashin Gaskiya ba. "Sarfraz inaso ka kalli wannan yaron dakyau, shin ka taɓa ganinshi? "Gaskiya ban taɓa ganinshiba! Wani abunne ya faru? Cewar sarfraz cikin dakiya. Girgiza Kai haidar yayi "you see ni dama nasan basu bane, kawai Idan zaku tafi ku tafi ni zan shiga gida inada abin yi, rantse rantse yaron ya Fara yi tare da cewa "baba na rantse da Allah shine ya bigeni, Allah ba karya nakeyi ba. Shi dai baban yaron ganin abinda ya faru sai ya yarda Cewa ba SARFRAZ bane, dakawa yaron tasawa yayi tare da cewa "Wuce muje! Nasan kila Wasu ka tsokana sukayi maka haka, shine Ni zaka zo kamin karya donka haɗani da makwabcina. Shikam sarfraz Har ya ƙosa yaje daki don yaba bandi labarin cewa yaudai haidar ya shigammusu faɗa. Shi kuma haidar mayar da kofar yayi ya rufe tare da wucewa nashi ɗakin... Aikam SARFRAZ na shiga daki ko zama beyiba ya fara ba bandi labarin abinda ya faru, harda kwatanta wa bandi yadda yaron yake rantsewa, shi ko bandi babu abinda yakeyi inbanda dariya... Hassu kumi tuni barcin gaske ya tafi da ita saboda cikin magungunan da aka bata a asibiti akwai na Barci.... Saukar C.A kenan a British airport, dayake dama Anan suke ajiye jet ɗin idan aiki ya kawosu England ɗin, wayarshi ya ciro yayi dialling ɗin number haidar Amma Abin haushi switch off, cab ya tara yace takaishi St Leo's Street. Cikin minti 15 suka iso ƙofar gidan haidar, sallamar me cab ɗin Aayaan yayi sannan shi ya nufi cikin harabar gidan, murmushi sosai ne a Fuskarshi na farincikin yau zasu samu lokaci mai tsawo Tare Da ɗan uwanshi su tattauna, kuma yasan yanzu in'sha Allah bazasu kumayin nisa da juna ba. Ya buga kofar yafi sau goma amma babu alamun an tawo buɗewa, tsaki Aayaan yayi don wani zubin be cika son jiraba barin idan Akwai abinda ya ƙagu ya samu, "Nasan sunanan tunda ga motar haidar ɗin a compound" Ɗan ƙara bugawa yayi saboda yayi tunanin ko basa kusa, dadai yaga alamun baza'a buɗeba sai ya samu wata kujera a cikin varendar ya zauna. Sai tsaki yakeyi gashi ya ƙara kiran haidar ɗin still numbershi a kashe. Ta cikin gidan kuwa haidar yanajin bugun, koma ince duka suna ji, amma gani sukeyi ko wannan mutumin ne ya dawo shiyasa suka ƙi zuwa su buɗe. A ƙalla Saida Aayaan ya kwashi Kusan minti 40 zaune a gurin amma babu su babu alamar su, duk haushi ya cika muyshi ciki, Gashi ya kira Number Aseey switch off, ta Nawaz kuma bata daukaba. Kuma miƙewa yayi da nufin ya ƙara bugawa idan basu buɗeba sai ya tafi asibiti ƙilan suna chan. Bugu uku yaji alamun an tawo buɗewa, aikuwa take yayi kicin kicin da rai "wato dama sunanan shine suka shanyani a titi. SARFRAZ ne ya buɗe ƙofar, ai kuwa yanayin ido biyu da Aayaan ya daka tsalle ya rungume shi, "Naji daɗin dawowarka yayana🥰, gaskiya yinin yau Ni mai Sa'a ne. Haidar dake tsaye gefen dining ne yaga sarfraz yaƙi dawowa, ai da sauri ya nufi kofar don kada yaje Mutanen dazu ne suka dawo. Yana isa yaga SARFRAZ ya ruƙunƙume Aayaan kamar zai koma cikin shi, ai kam da sauri shima ya washe baki don yasan wahalarshi akan SARFRAZ tazo ƙarshe. "Yoo! yaushe ka iso? Ai ya kamata ka sanar damu kafin ka tawo ko don mu haɗa maka wata kwaryakwaryar walima. Balla mishi harara Aayaan yayi "Gaskiya haidar wayarka batada amfani, ace kana Matsayin babban likita amma ka kashe waya hakanan, wato kai kazo gida ka kwanta baka tunanin al'ummar da suke jiranka. Kyalkyalewa da dariya haidar yayi "Auwo ashe kaima kaji yanda naji sanda naita kiranka inaso na faɗa maka SARFRAZ ya tashi amma taki shiga, Nima yau Ranar hutu nace don haka dole na kashe waya kada a dameni. Murmushin takaici kawai Aayaan yayi, tare da riƙe hannun SARFRAZ wanda sai yanzu ya sakeshi suka nufi cikin falourn. Babu kowa amma Akwai alamun ana kitchen ne, tunda ga kamshin abinci nan ya cika faloun. Ɗaya daga cikin sofa ɗin da suka zagaye falourn Aayaan ya samu ya zauna tare da cewa SARFRAZ "Bro kawomin ruwa! Hassu ce ta fito daga corner da dakinta yake sanye da hijabi, (tasa hijab ɗinne saboda kada haidar ko matar shi suga kumburin da wuyanta yayi. Da sauri ta ƙarasa kusa da Aayaan tana dariya tare da cewa "yaya sannu da zuwa! Gaskiya naji daɗi daka dawo. Dai dai nan sarfraz ya dawo riƙe da robar ruwa yana buɗewa sannan ya mikawa Aayaan. Kurɓar ruwan Aayaan yayi Sannan yace "hafsy, hafsy Nima Naji daɗi dana sameku lafiya, ina bandi? Dariya tayi me kyau sannan tace "inaga ko yana ɗaki nima Yanzu na fito. Shikam SARFRAZ ya zuba mata ido yana kallonta sai kuma ya Maida kallonsa kan Aayaan yace "yaya wai dama hassu hafsat yake nufi? "Au kai dama baka saniba? Cewar Aayaan yana kallon SARFRAZ da fuskar mamaki, Sannan ya ƙara cewa "ai sunayen da ake kiran me suna Hafsat dasu sunada yawa, kaga Akwai Hafsatul ikraam, akwai Hafsatu, akwai tatuwa, akwai hafsiyyah, akwai hansa'u, Akwai tatou hmmm sunada yawa ma. Buɗe baki SARFRAZ yayi "sunanki dama me dadine shine aka wani bata miki da Wani hassu, to nidai daga yau ikraam zan riƙa ce Miki. Dariya haidar yayi wanda fitowar shi kenan daga kitchen rike da tray ya cikoshi da snack's kala kala "to kai a matsayin ka na wa? Dazaka chanzawa ƴar Mutane suna? Murtuke fuska SARFRAZ yayi don beso Idan yana maganar hassu a riƙa sa mishi baki. Fitowar Bandi ce tasa kallonsu ya koma kanshi, domin tafe yake yana miƙa kuma yana hamma a tare, alamun yunwa ce ta tasoshi daga barcin. Ai cikin ƴan sakwanni idonshi ya washe Dalilin Aayaan daya hango, babu shiri ya karasa kusa dashi Tare da tsuguna yana dafa ƙafar Aayaan "bari na dibi albarka, yaya Yanzu ka dawo? Murmushi kowa yayi don abinda bandi yayi ya basu dariya, sosai aka samu guri aketa hira, itama Madam haidar ta fito aka haɗu akayi dinner tare gwanin ban sha'awa. Sosai suke ta hira, anan haidar yake ba Aayaan labarin abubuwan da sarfraz ya rikayi, har zuwa sanda Yan sanda suka tafi dasu.... girgiza Kai Kawai Aayaan yakeyi cikin ta'ajibi "Lallai sarfraz, yanzu da kaketa tsulawa Mutane Rashin kunya da ɓarna a gonakin su da sun kaika kotu fa? Charaf haidar yace "ai Wallahi Don Kawai suna ganin mutunci nane, amma nasan da badon niba Idan akwai abinda yafi lauya sai sun kira mutshi, nifa yanzu gaba ɗaya yabi ya zubar min da mutunci a cikin unguwar nan, duk masu ganina da mutunci saida ya tsokane su. Shidai Aayaan murmushin kawai yakeyi don yasan yanzu sarfraz ya koma dai-dai, kuma idan gobe suka isa gida wani mafarin farincikine ga ahalinsu duka. Madam haidar ce ta Kalli hassu tace "jita harda sanya hijabi yau, sai kace wata ustaziyar gaske, bayan duk Wata tsiya tare ake tsulata dake, naga wani zubin ko gyale Bakya rufe kanki dashi zaki bisu kuyita gararamba a titi. Sunne kai hassu tayi a cikin hijabi wai ita taji kunya. Kallon Aayaan madam haidar tayi tare da Cewa "wai kam kasan bayan ka tafi befi so Biyar suka zauna lesson ba? Saboda Tunda SARFRAZ ya warke komai ya tabarbare basa iyayin komai sai yawo da tsokane tsokanen fada gurin mutane.. Buɗe baki Aayaan yayi yana dariya, donshi abinma ya dena bashi mamaki "to shikenan idan muka koma gida zansa a nemi makaranta mekyau sai a maidasu. Haka dai suka cigaba da hira, daga a dauko chan sai a dauko nan, Basu suka ankara ba sai wajen ƙarfe shabiyu na dare, duk mamaki ne ya kamasu saboda ko magariba babu wanda yayi a cikinsu. Haka kowa ya tashi don yin sallar sannan su kwanta, anan ne sarfraz yace shifa a gurin Aayaan zai kwana. Murmushi Aayaan yayi yace "to muje mana meye na rikicin? °°′°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Tafe su umma suke ita da fauziyya misalin ƙarfe biyar na asuba don komawa gidan boka, dayake tun wancan Lokacin taketa buga-bugar inda zata samu kuɗin don aƙarasa mata aikin amma kuɗi yaƙi samuwa, yanzu ma dubu chasa'in ne ta samo su da kyar, suma Saida ta haɗa da saida wasu abubuwan nata tukuna suka kai yawan hakan, alamu ma ya nuna ko sallar asbah basu tsaya sunyi ba. Duba da lokacin aketa kiraye kirayen assalatu a ƙauyukan dake gefen inda suke. " Waiko fauziyya me kika cewa sale ne ya barki kika fito yanzu? "Ai umma cemai nayi jiya na baro ki hajaran majaran bakida lafiya, shine yace nayi sauri nazo na duba ki Kasancewar babu kowa dazai kula dake a gidan Daɗi umma taji, jin cewa sale da kanshi yace azo a duba ta, tasan ko banza anjima zataga saƙonshi. Yauma Saida suka tafiyu kamar babu gobe sannan suka isa bukkar bokan, lokacin har garin ya fara haske. Koda suka shiga cikin bukkar tarar dashi sukayi yanajan wani dogon charbi. Gyara zama yayi yana murmushi ganin su umma Domin be taɓa zaton za su dawoba duba da Tsawon kwanakin da aka ɗauka batare da sun dawo ba. Ciro kuɗin umma tayi tare da ajiyewa gabanshi, Sannan ta mishi bayanin cewa rashin samun kuɗin ne ya hanata dawowa, kuma ko yanzu ma bawai sun cika bane. Dariya bokan yayi tare da cewa fauziyya ta fita waje ta jirasu, fauziyya na fita ya matso kusa da umma yana washe baki "aida tun tuni kin faɗa min bakida kuɗi da bakisha wahala ba, domin akwai aljanin dazai shiga jikina ya kwanta dake sai ya bada kuɗin. Bata fuska umma tayi "kamar ya aljani ya kwanta dani? Inada aure fa! "Da gani ke Ƴar ƙauye ce, Don kinada Aure shine me? Mata nawa ne nayiwa aiki irin wannan kuma duk da auren nasu suka yarda. Shiru umma tayi tana tunanin Yadda zata yarda wannan baƙin ƙazamin ya kwanta da ita! Ta duba, ta duba amma taga bazata iya yarda ba. Cewa tayi "boka abar wannan maganar kawai gaskiya bazan iya ba! Kawai ka bari zan samo cikon. Wata uwar tsawa da ya rafka mata Saida ta firgice "mu muke magana kike Kawo mana naki tsarin? To maza ki tashi ki bani guri kafin na illataki. Daurewa umma tayi tace "to aikin nawa fa? "Baza'a yiba, ki tashi ki tafi nace. Daurewa umma ta daɗa yi ta kuma cewa "to kuɗin nawa fa, ka bani kuɗaɗen dana kawo maka. Wata sanda ya ɗauka yayi wasu iface iface ya saita umma da sandar aikuwa sai wasu tartsatsin wuta suka fara fallatsi, ai babu shiri umma ta miƙe ta fita da gudu, amma ina Saida wutar nan ta ƙona mata gefen ƙafarta. Fauziyya na ganin umma ta fito da gudu ta ƙarasa gunta da sauri tana cewa "umma ya akayi? An gama aikin? Kuka umma ta fashe dashi tare daba fauziyya labarin abinda ya faru, gashi inda wutar ta fallatsar mata sai wani irin zugi yakeyi mata har cikin kwakwalwarta. Da sauri fauziyya ta kama hannun umma suka ɗauki hanyar fitowa daga dajin dan abin tsoro yaba fauziya sosai, kafin su fita bakin hanya har ƙafar umma ta kumbura tayi sumtum da ruwa, bama ta iya ɗaga kafar sai dai janta takeyi. Namma sun daɗe tsaye a bakin hanya kafin su samu abin hawar da zai maidasu gida. Aikam suna isa gida umma ta samu gefen katifa ta kwanta tana jerawa boka tsinuwa. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Yauma dai zaune Nawaz take a saman gadonta tayi wanka tsaff abinta tayi kyau dukda ba wata kwalliya tayi a fuskar taba. Idan ta cinka daidai yaune Aayaan yace mata zai dawo randa sukayi wayar ƙarshe dashi, dukda shi yana kiranta Saidai bata ɗagawa saboda gudun Kada ya bata kunya, duk da haka kullum saiya Turo mata da messages sama da guda biyar. Duk na jaddada mata irin ƙaunar da yake mata da kuma ƙara tuna mata cewa ta shirya domin yana dawowa zasu angonce. Har wata fargaba takeji idan ta gama karanta messages ɗin, amma ko babu komai ya kamata ta sama mishi wani abin da idan ya dawo zata bashi a matsayin farincikin Dawowarsa, kuma aishi dayake yi mata ba wawa bane, kuma ance ka kyautata wa me kyautata maka. Tashi tayi cikin sanyinta ta nufi hanyar fita daga ɗakin tare dayin addu'ar Allah yasa kada ta haɗu da mummy. Cikin iKon Allah har ta shiga kitchen ɗin bata haɗu da kowa ba, duk abubuwan da tasan zatayi Amfani dasu ta Duba, Saida ta tabbatar ta haɗa komai tukuna ta fara aikinta a nutse. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Tunda suka fara shiri SARFRAZ ke cewa ya ƙosa su isa kodon yaga Nawaz, daga karshema kallon Aayaan yayi yace "yaya wai Kasan wacece Nawaz agurina kuwa? Girgiza kai Aayaan yayi yace "a'a brother bansaniba " Murmushi sarfraz yayi Tare da Cewa"itafa zan aura, Domin wallahi ina matuƙar kaunarta, yadda Kasan in hadiyeta haka nakeji. *DON ALLAH KUSANI A ADDU'A.* *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *56* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Wani irin tsinkakken miyau Aayaan ya haɗiye jin abinda SARFRAZ yace "wato yaron nan dai Akwai yarinta a Tare dashi har yanzu, in banda ma yarinta yaza'ayi ya Kalli Nawaz yace zai aureta? And kenan akwai damuwa idan muka isa gida" Abinda Aayaann ya aiyana a ranshi kenan. "Yaya Don Allah ina so idan munje ka roƙarmin Nawaz kace don Allah ta aureni! Cewar SARFRAZ Tare Da dafa kafaɗar Aayaan. Kallonshi Aayaan yayi Sannan yace "wai suk da kake wannan maganar dama ita Nawaz ɗin bata sonka? Shagwaɓe fuska SARFRAZ yayi Sannan Yace "wallahi yaya gani takeyi kamar Ni wawa ne, idan nace ina sonta har dariya take yimin wai ai ta girmeni, kuma don Allah yaya ba Mutum zai iya Auren Wadda ta girmeshiba? Shifa Aayaan abin ya Fara bashi tsoro, ganin SARFRAZ ɗin da gaske yake. Cewa yayi "eh mutum Zai iya Auren Wadda ta girmeshi, yin hakan ma sunnah ne, tunda Manzon ,Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya auri Sayyidatuna khadija kuma ta bashi shekara 15, amma Ni yanzu nafison ka auri wadda ke sonka da kanta ba wadda za'a matsa mata ba. Shiru SARFRAZ yayi tare da cewa "yaya kasan iyayena? Nayi missing ɗinsu sosai dasu da Yan ajinmu na makaranta , Kawai dai don ina London ɗin nan ne shiyasa ban damu da'a maidani gida ba, But inaso na gansu! Kada ka damu Zaka gansu in'sha Allah, kuma suma sunachan suna jimamin rashin ka, amma in'sha Allah yau komai zai zama tarihi. Cigaba da haɗa kaya SARFRAZ yayi saboda ATM ɗin da Aayaan ya bashi a hannuñshi ba karamin kaya ya siyaba shi dasu bandi da Hassu, yasai wasuma yace na Nawaz ne, harda mummy aka siyawa sarka da ɗan kunne, sosai yayi ɓarnar kuɗi. Shikam Aayaan dama Babu wasu kaya dazai shirya in banda back pack dinshi guda ɗaya. Waje ya fita Tare Da ciro wayarshi a aljihu, Number Mummyn shi yayi dialling, da Sallama ta ɗaga tachan ɓangaren, gaisheta yayi cike da ladabi yana tambayarta ya ta tashi? "lafiya lau Alhamdulillah". mummy tace. "Mummy Naga SARFRAZ! Kuma Yanzu haka muna Tare dashi... "Eye Aayaan! Kasan me kace kuwa? SARFRAZ fa kace? Ɗan ƴar uwata? "Eh mumy shi nagani, amma yanzu abinda nakeso shine zanyiwa securities ɗina magana, zasuzo su ɗaukeku su kaiku chan Zaria gidansu SARFRAZ ɗin, Nima gamunan yanzu zamu tawo.. Muryar mummy har ta Fara rawa "Aayaan ka turosu yanzu saimu tafi" kuma Don Allah ka kulamin dashi sosai. Tsabar zumuɗi bata ma tambayeshi suna inaba sukayi sallama ya kashe wayar. Faloun ya koma ya tarar su SARFRAZ har sun gama haɗa komai suna zaune alamun shi suke jira. haidar da madam Dinshi suma sun shirya dayake Tare zasu kaisu airport ɗin. Duk da Cewa sarfraz ba ƙaramin tashin hankali yasa haidar a cikiba na ɗan zaman da sukayi Tare, amma da zasu rabu Saida Kowa yaji Kamar ya zabga ihu, dama shi haka sabo yake (sabo turken wawa) hassu Harda ƙwalla taketayi Don ma tanata rufe idonta da mayafi. Ita kanta Madam haidar ɗin sai taji idonta yana kawo ƙwalla, amma tayi saurin gogewa saboda kada su hassu su lura da hakan. Allah ya taimaka suna zuwa jirgi na shirin tashi, a gurguje aka musu clearing ɗin komai suka shiga ciki, dayake Aayaan yafi zama a VIP, tsaff Hassu ta zage ta zama wayayyah kamar ba itaba, ko Irin ɗar dinnan ma batayiba. Madam haidar kam Saida suka koma gida gaba ɗaya ta kasa kataɓus, sai taga gidan yayi mata wani irin fili kamar an kwashe wani uban kaya masu yawa. Haidar keta kwantar mata da hankali (kada ki damu, kwanan nan zamuje ganin gida ai, duk zamu kai musu ziyara in'sha Allah, kuma ai dama haka baƙi suke, duk daɗewar da suka yi wata rana Dole za'a rabu, shiyasa Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam yace mu Mu'amulan cesu da kyakkyawar Mu'amula kuma mu kyautata musu) A haka dai ya samu ya kwantar mata da hankali. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Mummy kam tana gama waya da Aayaan ta samu Aseey tayi Mata magana akan maza su shirya ita da Nawaz Aayaan zai turo motoci yanzu akaisu zaria gidansu SARFRAZ. Ƴar fargaba ce ta kama Aseey "mummy meya faru haka da zamu tafi Zaria urgently? Yanzu muka gama waya da Aayaan wai yaga SARFRAZ kuma yanzu haka suna tare, zasu tafi chan Zaria ɗin. "Ikon Allah! To yanzu suna inane? Mummy tace "kedai kije ki shirya kayan naku na manta ban tambayeshiba, kuma kiyi sauri saboda Yanzu motocin zasu iso. Ɗakin Nawaz Aseey ta shiga ta faɗa mata cewa ta shirya yanzu zasu tafi Zaria. Sosai abin ya bata mamaki amma dayake batada bin kwakwkwafi bata tambayi Aseey meya faru dazasu tafi zaria yanzu ba, sai kawai tace "to" tare da miƙewa tana nufar wardrobe. Kaya kala uku ta zuba a cikin wata madaidaiciyar traveling bag, sai na jikinta guda ɗaya. Itama Aseey bata Wani dibi kaya da yawa ba, sai dai na muhsin ta ɗiba da ɗan yawa Saboda shi zai iya ɓata wa. Cikin abinda befi minti talatinba har sun gama shirin su sun dau hanya zuwa Zaria, kuma har a lokacin Nawaz na cikin duhu saboda ba'a faɗa mataba kuma bata tambaya ba. Ashley Kawai aka bari a gidan, dayake tana Chan tana barci har suka gama shiri, saida zasu fita ne Aseey ke cewa Mummy "Ashley fa tana ciki! "Shareta Kawai, Don bazani da itaba, idan ta tashi nasan zata nememu, idan ta kira a waya zan faɗa mata ta jiramu ko ta tafi, duk wanda takeso. Dayake yau babu Aayaan tare dasu ai kuwa securities ɗin suka samu dama sai uban falfala gudu sukeyi, kuma su mummy duk sun rufe windows sannan hankalinsu baya titi shiyasa ma basu lura ba, kuma har da yanayin motar, domin idan kana ciki Bama ka gane ana tafiya. Cikin ƙanƙanin Lokaci suka isa Kano, koda Aseey ta gansu saman gadar kwankwaso Saida abin ya bata mamaki, don bawani dadewa sukayi da fitowa ba.. Sosai suka ɗauki hanyar Zaria,bayan securities din sun tambayesu za'a tsaya ne? Mummy tace "a'a" Domin babu abinda ke zuciyarta a yanzu illa zumuɗi ganin SARFRAZ. Ita dai Nawaz tana gefen Aseey ta jingina kanta da bayan seat ɗin motar ta rufe idonta kamar tana barci. Karfe huɗu a cikin Zaria tayi musu, dayake sun rigada sun san gidan sai kawai suka sauka daga Express way suka koma cikin unguwa. Mamaki fal cikin Mummyn SARFRAZ, farin ciki ma ya hanata yin magana, sai dai kawai ta rumgume mummyn Aayaan tayi shiru. Cewa su Aseey da Nawaz tayi "ku tafi dakinku kuje ku samu kuyi wanka ku huta, yanzu zansa a Kawo muku abinci. Muhsin kam saiya choge waishi a gun mummy zai Zauna, tafiya sukayi suka barshi anan. Tunda suka shigo gidan ƙirjin Nawaz ke bugawa kamar Zai fito waje, ga wata fargaba data cika mata zuciya. "Yau fa Aayaann yacemin ze dawo, ko dai wani abunne ya faru? Dole Akwai wani abu domin Babu yanda za'ayi hakanan mu tawo Zaria ba tare da wani dalili ba. Ganin batada amsar duka wadannan abubuwan sai Kawai ta watsar da tunanin taci gaba da sabgar ta dukda bata dena jin faduwar gaban ba. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Su Aayaann kuma a Nnamdi Azikiwe airport dake abuja suka sauka, securities ɗin shi na Abuja ya kira, babu jimawa kuwa suka iso, nan suma suka ɗauki hanya Don zuwa Zaria. Hassu tunda taji cewa sun iso Nigeria sai ta riƙa jin gabanta na tsinkewa tare da tararrabin kada a rabata da sarfraz tunda Yanzu ya samu lafiya, Idonta Sai cika yakeyi da ƙwalla tana gogewa a fakaice.. Sarfraz kam harya gaji da zama, tun yana kalle kalle sai ya koma ya kifa kanshi a cinyarshi. "My brother ko baka farincikin dawowarka gida ne?" Aayaann ya tambaye shi tare da dafa gadon bayanshi "No bro inayi sosai ma, Kawai dai na gaji da zaman motar ne, cewar sarfraz tare da ɗagowa daga duƙon da yayi. Sosai Aayaann ya kalli Fuskarshi Sannan yace "kada ka damu mun kusa ƙarasawa kaduna, idan muka isa zansa a tsaya mu huta kuci abinci sai mu wuce. Ɗan murmushi SARFRAZ ɗin yayi. Sam Aayaan beji daɗin Ganin sarfraz ɗin a haka ba, sai yake Ganin Kamar idan suka isa gida Mummy zata tuhumeshi.. Gyaran murya Aayaan ɗin yayi Sannan ya fara magana. "SARFRAZ duk abinda kakeso a duniya inaso ka faɗa Min ko menene kuma ko nawa ne in'sha Allah, hardai befi ƙarfina ba nayi maka alƙawarin yi maka shi. Da sauri SARFRAZ ya kalli Aayaan "sir dagaske kake? Jinjina kai Aayaan yayi tare da cewa"Eh dagaske nake, kuma Alkawari nayi maka... Sosai sarfraz ya gyara zama "zaka kaini China? "Har India idan kana so" Zaro ido sarfraz yayi "woo ni woo ni, wayaga sarfraz a China? Kutmar!🤭 Sai dai kuji ina cewa "chan cheng wei, jiang xian miing🤣🤣🤣 Sosai Aayaann yayi dariya sannan yace "idan har kanaso, zan neman maka makaranta achan saika karanci Yaren china ɗin tunda naji ma ka iya! Kwal kwal SARFRAZ yayi da Ido Kamar zaiyi kuka sai kuma yace "Ni Wallahi Daddy nake tsoro, sam bayaso nayi nesa dashi, dakyar idan zai yarda ma, ita ma mummy bason na matsa kusa da itan takeyiba zugawa zatayi a hanani zuwa. Shafa kanshi Aayaan yayi, "ka manta Kanada Ni? Nace ka dena jin komai Ni zan zame maka kamar garkuwa ne a duka lamuranka. Hannunshi SARFRAZ ya sargafe dana Aayaan Sannan yace "promise me brother" "I promise" cewar Aayann yana murmushi. Sai misalin 7:30pm suka isa Zaria, tashinsu bandi da Hassu Aayaan yayi sannan suka nufi masallaci don bada farali. Duk ba yunwa sukejiba Kasancewar madam haidar ta haɗa su da kayan ciye-ciye kala-kala, komawa motar sukayi Sannan suka nufi gidan su SARFRAZ. Sosai SARFRAZ ya ƙosa su Isa gida, ganinshi a saman titin layinsu yasa yaji Kamar motar bata gudu, sosai zuciyarsa ke bugawa Kamar zata fito fili, duk abinda yake yi Aayaan yana lura dashi. Bandi ma daɗi yaketaji yau SARFRAZ zai koma ga ahalinshi a Matsayin me cikakkiyar lafiya, ita kuwa hassu kukane yake neman kwace mata, domin gani takeyi korarsu za'ayi, kuma ita ta rigada ta saba da Sarfraz, ta rasa meyasa takeji Kamar idan aka rabasu mutuwa zatayi.. Har cikin gidan suka shiga da motocin Kasancewar dama ansan da zuwansu... Alokacin Nawaz ta daɗe dayin barci saboda wani Irin ciwon mara daya kamata dalilin period da takeyi, shine Aseey ta saman mata Diclofenac tasha, bayan tasha ne taɗan samu relief har barci yayi gaba da ita. Mummy kuwa da Aseey sun kafa sun tsare a main falour yadda zasuji ƙarar shigowar motocin idan sun ƙaraso. Da gudu mummy tayo waje yayin da Aseey tayi dakin daddyn sarfraz saboda ya dawo wajejen magrib "mummy da Daddy pls ku fito gasu sarfraz sun dawo. Duka suka miƙe sukayi waje yayin da kowa na ƙoƙarin yadda zai isa zuwa parking lot ɗin, rungume suka tarar da mummy da sarfraz, sai zub da ƙwalla mummy takeyi tanajin zuciyarta kamar mumtaz ɗinta ta rungume.... Sosai Aayaann yake murmushi saboda yadda yaga ƙaunar sarfraz tsantsa cikin zuciyar Mummy, mamaki abin ya bashi ganin ga kowa amma babu Nawaz, yana so ya ganta kafin sarfraz ya ganta. Mummyn Aayaan na sakinshi mumynshi ta rungumeshi, gaba ɗaya sun babbake sun hana Daddy koda hannunshi ya riƙe.... Ko su hassu ba'a lura dasuba sai daga baya, shi kuwa sarfraz sai ya zama mutun mutumi ganin wasu tare dasu kuma yana ganin alamun kamanshi a fuskarsu gashi kuma be taɓa ganinsuba. A haka dai suka isa main falour ɗin, aka zazzauna, nan mummy ta bukaci jin a ina Aayaan ya tsinci Sarfraz. Aayaann ya fara basu labarin tun randa haidar yazo ya kaishi kauyen su hassu har zuwa kaisu England dayiwa Sarfraz aiki da kuma dawowarsu.. Daddyn sarfraz ne ya numfasa Sannan yace "Lallai Aayaan kai kyauta ce daga Ubangiji Allah, waye zai iya irin wannan sadaukarwar? Irin wannan kashe kuɗi Haka, lallai kai ɗin na daban ne, kuma in'sha Allah zaka gama da duniya lafiya. Godiya sosai da addu'oi Daddy yayita yi mishi. Shikam SARFRAZ jingim yayi yana ganin shikuwa mezaiyiwa Aayaan ya biya shi Irin wannan sadaukarwar da yayi mishi, kuma gaba ɗaya ya shiga rudani akan Aayann ɗin wanene a gurinshi. Kamar Daddy yasan me sarfraz yake tunani, kallon sarfraz yayi yace "kasan wadannan su waye a wajen ka? Girgiza kai sarfraz yayi tare da cewa "daddy ban saniba Amma dai yaya Aayaan yace shi yayana ne! "Tabbas shi yayan kane kuma me kaunarka ta haƙiƙa, domin halin daka shiga ba ƙaramin tashin hankali zamu fuskanta ba da munganka a lokacin, amma saboda hankali da tunani irin na Aayaan ya gwammace ya ɗauki komai nadaga tashin hankali da damuwa har zuwa kisan maƙudan kudade shi kadai, tabbas bakada kamarshi.... Labari Daddy yakeba sarfraz na aurenshi shida muntaz har zuwa sanda ta haifi sarfraz ɗin da kuma mutuwarta, gaba ɗaya falourn yayi shiru bakajin komai face saukar zuciya a hankali, duka kuwa idonsu cike yake da ƙwalla, barin mummyn sarfraz da Mummyn Aayaan. Cigaba Daddy yayi har zuwansu mummy da bayyanar ita ɗin tagwayen muntaz ce, zuwa lokacin SARFRAZ yayi kuka har ya gaji, gaba ɗaya ji yayi Duniyar tayi mishi zafi ta ina zai soma rayuwa da sanin cewa ba Mummy bace Asalin wadda ta haife shi ba, ga wani irin girmanta daya ƙara cika mishi zuciya, lallai ita ɗin ta kwarai ce, don be taɓa fuskantar wani abu daga garetaba wanda zai nuna cewa ba ita ta haife shi ba.... Yanzu baida wani hope a rayuwarshi, ji yake komai nashi ya rushe, da sauri ya miƙe tare da cewa "ina Nawaz? Yaya Aayaann yace min anganta, don Allah Kada kucemin ba'a gantaba! Murmushi Daddy yayi "ka kwantar da hankalinka anga Nawaz yanzu haka tana cikin ɗaki tana barci, bata jin dadin jikinta ne. Aida sauri SARFRAZ yace daddy don Allah ka aura mini ita nan da sati daya, wallahi ina sonta, kuma bazan iya rayuwaba idan babu ita. Sannan yayi Hanyar ɗakin cikin hanzari don yaje ya ganta.. Daga Aayaan har hassu babu wanda zuciyarshi bata buga ba, Aayaan kam har wani tuƙuƙin wuta ne yaji ya maƙale mishi a wuya. Mummy kam harta fara hasashen yadda zatasa Aayaan ya saki Nawaz ɗin don SARFRAZ ya aureta jin yace bazai iya rayuwaba idan babu ita. Da sauri daddy ya dakatar da Sarfraz kafin ya ƙarasa ɗakin "SARFRAZ sai dai kayi hakuri domin Yanzu Nawaz matar aurece! Cikin wani irin vibration safraz ya waigo Tare Da cewa wane ɗan kutumarrrrr uba ne ya auremin mata? To wallahi koda shine sarkin duniya saiya saketa, na rantse da Allah be isa yayi min wannan yankan kaunar ba, Nawaz ɗin tawa? Wallahi banida lafiya ne, ina buƙatar addu'oin ku masoya Sannan ina jiran comments da sharhi, yadda banida lafiyan nan na daure nayi muku typing kuma ku daure kuyi comment da sharhi. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *57* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* "Ƙaniyarka Sarfraz! Nace ƙaniyarka!!, Kanada hankali Kuwa? Kallon Aayaan dady yayi sannan yace "Wai Aayaan nikam kodai yaron nan ya samu wata matsalar ne a kwakwalwa dadilin ciwon da yayi? Kasancewar Aayaan ɗin nada shekaru kuma ya karanci rayuwa sai ya zamana koda ka kalleshi bazaka taɓa gane yana cikin tashin hankali ba, amma a baɗini kuwa shikadai yasan Yadda zuciyarshi ke tafarfasa. "Daddy Allah duk gwaje gwajen da za'ayi anyi kuma an tabbatar kwakwalwar shi ta koma normal babu wata matsala. "Eh Lallai! kenan iskancine yasa yake ƙunduma min ashariya a cikin gida, to Wallahi Sarfraz ka kiyayeni! saboda kai ɗan Gwal ne shiyasa mijinta zai saketa kai ka aureta, kuma naga ai Allah dakanshi yace saki halal ne amma bayasonshi. Wato saboda wani shirmen banzan ka sai ayi abinda Allah bayaso Koh? Aseey kam haushin sarfraz ne ya kamata, "wato a saketa! to sannu ɗan lu'ulu'u, idan ba lu'ulu'u ba taya Muna murnar munsamu gwarzuwa kazo zaka ja mana jarfa" abinda Aseey ke tunani a zuciyarta kenan, daga karshe ma tace "ka mutu mana! Ka daɗe baka mutunba, ya gama wahala dakai shine zakazo kuma kana ƙunduma mishi ashariya, don kaga yarinya gwanin kyau, ga komai da komai shine kake ganin da kai ta dace". Mummyn sarfraz ce tace "haba fabulous meye kuma na zagi bayan kana kallon manya a gabanka, ai Nasha kai me hana wani ne idan kaji yanayi". Ita kuwa hassu ji tajeyi kamar ta zunduma ihu, yanzu Sarfraz wata zai aura ya manta da ita kenan, shidai bandi zaune yake yana kallon ikon Allah. Mummyn Aayaan kam tayi nisa cikin tunanin yadda zatasa Aayaan ya saki Nawaz ɗin salin alin, domin ita kallon sarfraz takeyi a matsayin mumtaz ɗinta, kuma duk duniya babu Abinda take ganin bazata iya yiwa mumtaz ba. Ɗan ɗaga murya Aayaan yayi "sweet bro dawo, zo gurina, ka manta alƙawarin da mukayi nida kai? To yau zan fara amfani dashi. Takowa Sarfraz yayi ya dawo gaban Aayaan ya tsaya. "Ka tabbatar kana ƙaunar Nawaz? kuma zaka iya zama da ita har ƙarshen rayuwarka? Aayaann ke tambayar Sarfraz yana kallon Cikin idonshi. "Eh yaya, wallahi ina matuƙar ƙaunarta! Sarfraz yace shima yana kallon Aayaan ɗin. Miƙewa Aayaan yayi Tare Da cewa "Aunty Aseey zo muje, kaima Sarfraz tawo." Mummyn Sarfraz ce tayi sauri ta miƙe Tare da cewa "kul Aayaan! Kul nace! Kada ka sake kayi abinda bashi bane, kadaiji na gaya maka. Shima daddy cewa yayi "laillai Aayaan! Ina kallonka a matsayin me hankali, taya zakayi abinda Allah ma zaiyi fushi damu? Kwantar da kai Aayaann yayi Tare Da cewa "Dad and mum pls trust me! I will never do something that all of us will regret, but I'm just trying to do something that will be a way to both of us. Shiru kawai duka sukayi basuce komai ba, amma zuciyarsu na ɗan bugawa kada fa Aayaann ya saki Nawaz, ita kuma Mummy addu'a takeyi akan Allah ma yasa Aayaan ɗin ya haƙura da Nawaz ɗin ne. Fita harabar gidan Aayaan yayi, Aseey da sarfraz suna biye dashi a baya har zuwa wani gefe inda aka Wadata da hasken lantarki duba da Lokacin dare yayi sosai "SARFRAZ inaso ka saurareni dakyau, yanzu zansa Aseey taje ta tawo da Nawaz nan gurin, Ni zan matsa inda bazata ganni ba. Inaso ka tambayeta shin zata iya aurenka ta zauna dakai a matsayin miji? Ni kuma wallahi nayi maka alƙawarin har dai tace eh to Wallahi saika aureta duk wuya duk rintsi. Murmushi SARFRAZ yayi "to yaya Nagode sosai, zan tambayeta. Aseey kuwa baƙin cikin daya cika mata zuciya ji takeyi kamar ta kama SARFRAZ da duka, amma in'sha Allah tasan babu yanda za'ayi Nawaz ta yarda da wani SARFRAZ bayan tasan Aayaan mijin tane. Tun kafin Aayaan ɗin ma yace taje ta kira Nawaz ta juya don kiranta, da sauri sauri ta isa falourn zata buɗe kofar dakin da Nawaz ke barci a ciki, dad ne ya kirata "zo nan Asiyah!" Gaban dad Aseey ta ƙarasa tare da cewa "daddy gani" "Asiyah ke babba ce, ko babu komai kin girmi Aayaan kuma kinyi aure har kin haihu, nasan ko iya nan aka tsaya za'a saki a jerin waɗanda suke da cikakken hankali kuma suka san babin rayuwa, don haka nake roƙo a gareki don girman Allah kada ki bari Aayaan ya saki Nawaz, idan kuma har ya saketa to bazan bashi laifin shi kaɗai ba, Wallahi har dake zan kalla da abin kuma bazan taɓa bari SARFRAZ ya auretaba har abada Kinga kenan kinjawa yarinya bata jiba bata ganiba. Sosai Aseey taji maganar tayi mata nauyi kamar an ɗaura mata wani dutse ne akanta ga kuma wani irin bugawa da zuciyarta Keyi, "to Daddy in'sha Allah hakan bazai faruba. "To Asiyah Nagode, Allah yayi miki albarka!. "Ameen dady Nagode" Aseey tace tana kai dubanta gefen dasu Mummy suke zaune, gaba dayansu sunyi tagumi hannu bibbiyu, kana kallonsu zaka gane suna cikin tashin hankali mai girman gaske. Ita Mummyn SARFRAZ tana addu'a Allah yasa kada Aayann ya saki ƴar mutane saboda Sarfraz, ita kuma Mummyn Aayaan tana tararrabin ya za'a ƙare da Sarfraz idan Aayaan yaƙi sakin Nawaz? Wucewa tayi zuwa Dakin, gaba ɗaya sai take jinta babu nauyi, ga duka gwuiwowinta sun sage, a zaune ta Tarar da Nawaz ɗin alamun yanzun ta tashi daga barcin, domin idonta ma be gama washewa daga barcin ba. "Sister kin tashi?" Aseey tace tana ƙarasawa gefen Nawaz tare da zaunawa. Murmushi Nawaz tayi "Eh Aunty na tashi, ina muhsin? "Muhsien yayi barci, ya jikin naki?. "Da sauƙi aunty, Nagode da nuna kulawa. Kada ki damu ai kedin yar uwata tace, burina kullum na ganki cikin farin ciki da walwala. Gyaran murya Aseey tayi sannan taci gaba da cewa "Nawaz! Ina ƙaunarki, mummy tana ƙaunarki, ƙanina AAYAANN yana ƙaunarki kuma muhsien ma yana ƙaunarki, Don Allah Nawaz muma ki ƙaunacemu koda na second ɗaya ne! Ayanzu Aayaan bashida sauran farincikin daya Wuce ke, tunda nake ban taɓa ganin Aayaan yaso wata ba, kuma ban taɓa jiba face a kanki, Nawaz don Allah ki zama ƴar halal ki maida Alkhairi ga wanda yayi miki Alkhairi. Gaba ɗaya Nawaz ta shiga rudani, ta rasa meyasa Aseey keyi mata wadannan maganganun, numfasawa tayi sannan tace "Aunty nayi miki alkwari bazaki taɓa yin kuka daniba, Sannan nima ina ƙaunar ku kamar Yadda kuke ƙaunata, kuma a yanzu banida wani family da nake kusa dashi kuma suke nunamin ƙauna kamar naku familyn, And Game da yaya Aayaann ko naƙi Allah bazan taɓa watsa mishi ƙasa a ido ba, domin shidin ɗan halal ne kuma ya nunamin halalci. Farinciki ne ya mamaye Aseey jin abinda Nawaz tace, tasan in'sha Allah Yanzu batada wata Matsala tanada tabbacin Nawaz bazata yarda ta amshi Sarfraz a matsayin masoyi ba. Hannun Nawaz ta haɗa da nata guri ɗaya, "Nawaz Nagode! Nagode!! Allah ya saka da Alkhairi, Allah ya shiga lamuranki, kuma ya ƙara mana danƙon ƙauna. Murmushi Nawaz tayi tace "Ameen Aunty, Nima Nagode " Yanzu ki ɗauko hijab ɗinki kizo muje in nuna Miki wani abin farin ciki da Aayaan yayi saboda ke. Mikewa Nawaz tayi ta karasa inda ta ajiye hijab ɗin ta ɗauka "to Aunty muje in gani! Mikewa Aseey itama tayi sannan tace "muje sister" Koda suka fito faloun babu kowa kasancewar Daddy ya tashi sai Mummy ta nunawa hassu ɗakin baki tace ta shiga shikuma bandi tace yaje ɗakin SARFRAZ, Sannan su suka tashi suka shiga ciki. Har cikin harabar gidan Aseey ta rakata Sannan tace "ki tsaya anan zakiga abin dana faɗa Miki, Sannan kuma kome zakiyi kada ki manta akwai haƙƙin auren wani a kanki. Sannan Aseey ta juya ta koma baya, amma bata shiga Cikin ɗakin ba ta laɓe a gefe saboda ganin me zai faru. Nawaz na tsaye taji an dafata ta baya, cikin sauri ta juya don ganin waye? Ai Saida numfashinta ya tsaya na wucin gadi sannan ya dawo, baya tayi zata faɗi tsabar ruɗani, ai kuwa da sauri Sarfraz ya tareta ya dawo da ita. Zaro ido tayi "Sarfraz kaine? Ko dai gizo kakemin? Don Allah kaine? Murmushi yayi "nine malama, ba gizo nake yimiki ba , buɗe hannunshi yayi alamun tayi hugging Dinshi. Shiru Nawaz tayi tana tunani "tabbas sarfraz ya cancanci na rungumeshi ko don farincikin ganinshi da dawowarshi da rai da nayi a Yanzu, amma haƙƙin auren dake kaina fa? Tabbas idan na rungume Sarfraz kamar naci amanar Aayaan ne tunda aure dai aure ne koda ta wace hanya aka ɗaura shi. Basarwa tayi "Wato ka dawo zaka cigaba daga inda ka tsaya ko? Rimi-rimi yayi da ido " haba Sweet heart Yanzu hug kadai kin kasa yi min? Ko bakya farin cikin dawowata ne? Zaro ido Nawaz tayi cikin mamakin kalamansa "haba sarfraz nasan duk duniya babu Wanda zai fini farincikin dawowarka Idan aka cire iyayenka, Sarfraz Ni nasan irin halin dana shiga bayan bakanan, Nifa har burin mutuwa saida nayi, nayi kukan zuciya nayi na fili har Saida zuciyata ta ƙeƙashe, kuma duk sanda zan tuna dakai kaina nake ba laifi. Daɗi ne ya ziyarci zuciyar Sarfraz ganin akwai alamun Nasara, to shikenan nabar hug ɗin, amma to ko One kiss ki bani mana! Ina so naji ɗumin jikinki ta yadda zan yarda cewa kece a gabana Namma dai Nawaz murmushi tayi "hmm ashe dai me hali baya manta halinshi, nidai yanzu ka bani labarin abinda ya faru bayan mun rabu, ta faɗi hakan ne Saboda ta kawar da Maganar kiss ɗin. Gefen inda aka zagaye Flowers ya samu yace ta zauna sannan shima ya zauna, "Nawaz nashiga tashin hankali da damuwa bayan an tafi dake, cigaba yayi da bata labari har zuwa sanda ya farka ya dawo hankalinshi, kuma ya bata labarin su hassu da bandi da kuma wahalar da sukasha dashi sanda baya cikin hayyacinshi. Sosai Nawaz taji wani girman Aayaan ya kuma cika mata zuciya jin cewa ta dalilinshi akaga Sarfraz, kuma be tsaya iya nanba ya kaishi har ƙasar waje don neman lafiyar shi, ga tausayinshi ya ƙara kamata , wato shidai babban mutum daban yake, basai dole a shekaru ba. sannan a yanayin Labarin taɗan lurada Sarfraz ya damu da hassu sosai, kuma itama taji ƙaunar hassun ta cika mata zuciya dukda bata ganta ba. Cewa tayi "masha Allah" tare da goge ƙwallar data ke zubowa daga cikin idonta "sarfraz lallai mun fuskanci jarabawa me girman gaske amma ga Dukkan alamu munyi nasarar cinyeta, kuma naji daɗi da Allah ya kuma haɗa mu cikin inuwa ɗaya, Sannan ina fatan mu kasance a haka har gaban abada. Daɗi sosai SARFRAZ yake ji don a ganinshi Nawaz tana nufin su kasance tare har abada ne ta Hanyar aure. Bashi labarin bayan sun rabu tayi saidai Koda wasa bata faɗa mishi cewa Aayaan bane ya taimaka mata kuma bata ce mishi anyi mata aure Ita da Aayaan ba. Shiru SARFRAZ yayi yana duba wannan lamari, "Lallai Nawaz ta shiga gararin rayuwa, Amma komai yazo ƙarshe tunda gani na dawo". Hannuwanta ya kama tare da marairaice murya "malama Don Allah zaki aureni? PLS ki taimaka Min mu zama abu ɗaya, Wallahi ina ƙaunarki Fiye da yadda kike tunani, sannan nayi miki alkawarin zaki kasance cikin farin ciki har ƙarshen rayuwarki muddin kika aureni. Kwace hannuwanta Nawaz tayi Tare da ja baya "Sarfraz wai har yanzu bazaka dena wannan Labarin ƙanzon kuregen naka ba? Wai tayaya ma zan aureka, ya kamata ka gane niba tsarar aurenka bace, shekaruna sunfi naka, kuma Ni banada ra'ayin Auren Wanda na girmeshi. Da sauri Sarfraz ya ƙara matsawa kusa da ita da niyyar hugging ɗinta sai tayi sauri ta goce tare da nuna mishi yatsa "SARFRAZ wallahi ka kiyayeni kada ka sake ka kuma taɓa min jiki, wai ina wasa dakai ne. Banza yayi da ita ya nufeta gadan gadan, ganin Idan ta tsaya zai rungumeta da gasken ne yasa tayi Hanyar ɗaki da gudu. Cikin hanzari SARFRAZ ya riƙe hijabinta yayo baya da ita, ai kuwa take wuyan hijab ɗin ya yage sakamakon yadda ya jashi da ƙarfi, sauka hijab ɗin yayi saman kafadarta. Sai sannan Sarfraz ya tsaya Yana ƙare mata kallo, gani yayi kamar ba Nawaz ba, ta ƙara kyau kuma kamar tayi ƙiba. Hannu yasa ya tuge hijabin gaba ɗaya Daga jikinta. Rufe idonta tayi tana cewa "wai SARFRAZ Meye haka? Bakada hankali ne, meye zaka ciremin hijabi. Binta yayi da kallo, tabbas Nawaz ta chanza sosai, to ko dai Daddy da gaske yake dayace tayi aure. Baya takeyi yana binta, "Nawaz wai aure kikayi da gaske? Cikin tsiwa Nawaz ɗin ta buɗe idonta tace "eh Aure nayi sai me? Saboda abubuwan da yake mata sun fara kaita bango. Take idanuwan Sarfraz sukayi jajir, finciko ta yayi ya matseta a ƙirjin shi yana cewa "Wallahi be isaba ko waye shi, taya zai kai kanshi gonar daba tashi ba? Na rantse da Allah dole ma ya sake ki, don ke ɗin mallakina ce kuma don ni aka halicceki, kici kicin kwacewa Nawaz takeyi shikuma ya samu damar haɗe bakinsu guri ɗaya. Ai da sauri Nawaz ta chafki leɓen shi na ƙasa ta gatsa mishi cizo, da sauri ya saketa saboda azabar data ziyarci kwakwalwar shi. Ganin ya saketa ita kuma ta arta a guje ba tare data gane ina tabi ba, shima rufa mata baya yayi, don ya kudiri niyyar idan taƙi bashi haɗin kai ya aureta ɗaukarta zaiyi ya gudu sai dai Duk Abinda zai faru ya faru. Firgici ne ya kama Nawaz ganin ta da tayi a bakin gate, da sauri ta fara Neman yadda zata buɗe gate ɗin, domin ta gwammace ta fita a haka data tsaya Sarfraz yayi Yadda yaga dama da ita, don anata gani takeyi zai iya yin komai duba da Yadda idonshi ya kaɗa yayi jajir. Dai dai lokacin shikuma Aayaan ya dawo Daga waje saboda bayan Aseey ta shiga kiran Nawaz colonel ya kirashi a waya kuma ya zamana baya jinshi alamun network Babu kyau, shine ya fita waje saboda ya samu service. A jikinshi ta faɗa tana cewa "yaya Aayaann don Allah kada ka bari ya taɓa Ni, Wallahi bashida kunya. Shikam Sarfraz saiya tsaya yana ganin ai kaman Nawaz takai kanta gida ne, tunda yasan Aayaan zai ribaceta ta aurenshi. Daɗi Aseey taji ganin Aayaan ya shigo gidan, don gaba ɗaya mamakin rashin kunyar Sarfraz takeyi, "yana kallon wannan garɓasheshiyar macen yace zai hake mata. Kuma daɗin dataji na biyu daya kasance Aayaan bega duka abinda ya faru ba, tasan shi namiji ne, dole idan yagani ranshi zai ɓaci. Maida gate ɗin Aayaan yayi ya rufe "to ki sakeni" yace yana kallon Yadda ta ruƙunƙumeshi Kasa sakinshi tayi tana cewa "yaya Aayaann don Allah idan na sakeka kada ka barshi ya matso kusa Dani. Shi abinma dariya yaso bashi don Yadda Nawaz ta dage bilhaƙƙi ita tsoron Sarfraz takeyi. "Okay to kada ki damu bazai taɓa kiba" Sakinshi tayi a hankali tana kallon inda SARFRAZ ɗin yake a tsaye, murmushi yaketa yi ya zuba mata ido. Harara ta balla mishi sannan ta kauda kai daga kallonshi. "SARFRAZ meya faru haka naganku Kamar masu dambe? Aayaann yace yana kallon sarfraz ɗin. " Yaya wai kawai don nace ta taimaka ta aureni shine tace ita wallahi bazata aureni ba, wai ta girmeni kuma ita batada ra'ayin Auren Wanda ta girma. Kallon Nawaz Aayaan yayi sannan yace "wai hakane? Ɗaga kai Nawaz tayi alamun eh, "to meyasa bazaki auri Wanda kika girma ba? Naga ai sunnah ne? Aayaann ya kuma tambayar ta Ni kawai bazan iya shirme bane, wai taya ma zan auri wanda shi kanshi be iya control ɗin kanshi ba, to taya kenan Ni zaiyi controlling ɗina? Kuma kaima naji ai sunnah kace ba farillah ba. Dariya ce taso kwacewa Aayaan ɗin, yadda Nawaz ta dage tana koro jawabai, yau ko kunyarshi da take ji ma babu. Shanye dariyar yayi Saboda kada su maida abin wasa, "to yanzu ya kukeso ayi? SARFRAZ ne yayi saurin cewa hakanan zata haƙura ta aureni, aiba shekaru zata duba ba ƙaunar danake yi mata zata duba, kuma naga ai aure ibada ne sann...... Ai Nawaz bata bari ya gama faɗar abinda zai faɗa ba tace "nifa ban yarda ba Wallahi, kai bari kaji ma nifa da in aureka gara na mutu single. Sosai dramar take ba Aayaan dariya amma yana ƙoƙarin saita kanshi, it means yanada rabon zama da Nawaz kenan? Tunda gashi ita bilhaƙƙi taƙi yarda da batun Sarfraz. "To yanzu abinda za'ayi muje kowa ya samu ya kwanta tunda kunga dare yayi sosai, da safe saimu ƙarasa maganar Koh? Sarfraz beso Hakan ba, amma dayake yanada hope a gurin Aayann saiyace to Allah ya kaimu. Itama Nawaz sai tace "to", koda suna tafiya zasu koma cikin ɗakin bata bari SARFRAZ ya matso kusa da ita ba, tana gefen Aayaan. A falour suka tarar da Aseey zaune a kujera tana danna waya. Kallon Nawaz tayi tace "kinga surprise Koh? Kauda kai Nawaz tayi ta shige ɗaki Don yanzu gaba ɗaya ma haushin sarfraz takeji, tama rasa murna takeyi ko akasin ta. Ɗakin SARFRAZ su Aayaann suka wuce, anan suka tarar da bandi har yayi barci, "tashi kayo alwala muyi sallah" Aayaan ya cewa SARFRAZ shima ya miƙe ya ƙarasa bayin donyin alwalar. Sallah sosai sukayi Aayaan yana addu'ar Allah ya zaɓa musu abinda yafi Alkhairi, shikuma Sarfraz gani yakeyi ai babu Alkhairin daya wuce ya samu Nawaz a matsayin mata. °°° Koda Nawaz ta shiga ɗaki sai Aseey ta miƙe ta shiga ɗakin baƙi ta tawo da hassu suka shiga dakinsu don kwanciya. Sakalo hassu tayi tana kallon Nawaz, tasan tafita komai bazata iya ma haɗa kanta da itaba, amma kuma cikin ikon Allah ko kaɗan bataji tanajin haushin Nawaz ba, sai jima da tayi tana ƙaunarta. Itama ta ɓangaren Nawaz ɗin sai taji tanajin tausayin hassu ɗin, gata ƙarama kuma a haka tayita jigila da sarfraz. Sosai Aseey ta ƙara ganin hankalin Nawaz, Yadda Sam taƙi yarda farin cikin ganin SARFRAZ ya rufe mata ido tayi abinda bashi bane. Ko hirar ma basu samu sunyi ba kowa yayi barci kasancewar dare yayi sosai kuma duka a gajiye suke. Haka da safe ma a makare suka tashi, lokacin ma Mummy ce tazo tace Musu su fito Daddy yace yanada zama da za'ayi a main falour, shine ta tashe su. A gurguje suka shirya Sannan suka tafi zuwa mai falour ɗin, Anan suka tarar da kowa zaune saboda dama su kadai ake jira. Addu'a daddy yayi Sannan yace "haƙiƙa sarfraz kabani mamaki, ban taɓa tunanin zakayi haka ba, Yanzu abinda kayi shine godiyar da zaka yiwa Aayaan na duka Alkhairin daya yi maka? Ɗago kai Sarfraz yayi yana kallon dady da alamun tambaya a Fuskarshi. Sosai dady ya karanci hakan a fuskar SARFRAZ ɗin. "Nawaz dai ba kowa bane mijinta illah Aayaan, kuma a gabanshi kake duka rashin Mutuncin da kakeyi, kuma ka ƙara da cewa koshi waye saiya saketa. Yanzu gashinan saiya saketa ka aureta. Zumbur sarfraz ya miƙe yana zare ido tare da nuna Aayaan bakinshi na motsi alamun yanaso yayi magana amma ya kasa. Nagode da addu'oin ku, Allah ya saka da Alkhairi kuma yabar ƙauna. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *58* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Chigaba da nuna Aayaann ɗin yakeyi still bakinshi na motsi, kowa na falourn binshi yake da ido yana tunanin me zai yi. Juyawa yayi ya ruga da gudu zuwa dakinshi ya faɗa akan gado, sai Sannan ya samu damar fitar da abinda yakeso ya fitar tun ɗazu "innalillahi wa'inna ilaihiraji'un! Lahaula wala quwwata illah billah, wai meyasa tun farko ban tambayi waye mijin nataba? Yanzu haka nasan Nagama ɓata kaina a gurin yayana, meyasa idona ya rufe haka? Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un yanzu ya yake kallona? Fashewa yayi da kuka yana girgiza kai. "Na barta! Wallahi nabar Nawaz har abada koda ita kadai ce macen data rage a duniya. Alkhairin yaya Aayaann a gurina ya Wuce wai in tsaya ina wani shirme akan mace. A chan falour kuma bayan Sarfraz ya ruga da gudu shima Aayaan saiya tashi da sauri zai bishi, Daddy ne ya dakatar dashi "Muhammad kull, kada ka sake ka bishi! Kyaleshi. Abin duniya duk ya ishi Nawaz, gani takeyi Kamar kowa zai tsaneta Tunda kusan duk don Ita hakan ta faru. Mamaki ne Ya kama kowa ganin SARFRAZ ya fito yana tafe yana tangaɗi idanuwanshi duk sun kaɗa sunyi ja, a gaban Aayaan ya tsaya Tare Da zubewa kan gwuiwowinshi Sannan ya duƙar da Kai "yayana Don darajar Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama ka taimaka ka yafemin, Wallahi Ni butulu ne kuma na cika mai son kans....... Dakatar dashi Aayaann yayi "yi shiru, kada ka kuma neman yafiyata, ni baka yimin komai ba. Daddyne yace "kyaleshi ya fitar da duk abinda ke zuciyarshi tanan ne zan gane idan da gaske yake ko kuma so yake yayi wasa da hankalinmu domin naga ya chanza daga Sarfraz ɗin dana sani. Wani irin ihu sarfraz ya saki "Daddy wallahi ban chanza ba, don Allah kuyi hakuri! Wallahi na haƙura da Nawaz har abada kuma wallahi dad tun sanda kace matar yaya Aayaann ce Naji duk wani abu danakeji game da ita ya goge, wallahi Ayanzu kome zai faru bazan taɓa iya aurentaba, girman yayana ya shafeta, Ayanzu Ita ɗin Aunty nace. Mamakine ya kama kowa dake falourn "Ashe Sarfraz akwai sauran hankali a tare dashi, kenan shima ya fara shiga shekarun Dattaku, shikam Aayaan sai Sarfraz ɗin ya bashi tausayi yanda ya nuna yana matuƙar ganin girmanshi. Ita ma Nawaz ji tayi kamar sarfraz ɗin ya tsamotane daga cikin ruwan ƙanƙara yasaka ana ɗumi. Mummyn Aayaan kam tafi kowa murna, Domin bataso ta rasa Nawaz a Matsayin suruka sannan a lokaci ɗaya kuma bataso Sarfraz ya shiga ƙunci na rasa abinda yakeso saboda nata kwanciyar hankalin. Daddy ne yace "zo ɗan albarka! Ni dama nasan mummynka ta baka tarbiyya me kyau, ayau kuma nayi alfahari da ita da Kai gabaki ɗaya, zo ka zauna kusa Dani. A hankali SARFRAZ ya karasa kusa da Daddy ya zauna, rungumeshi Daddy yayi yana cewa Allah yayiwa rayuwarka Albarka kaida ɗan uwanka, Naji daɗin yanda ka nuna cewa kasan halalci. Fashewa SARFRAZ yayi da kuka, Daddy idan banyiwa yaya Aayaann halallciba babu wanda zan taɓa yiwa halalci a rayuwata, shiya zamemin garkuwa a rayuwata sanda na rasa Komai da kowa, kuma shiya nunamin me kalmar ɗan uwa take nufi, ya sadaukar da dukiyarsa a kaina mara adadi duk dan in samu lafiya. Kuma shidin yayanane saboda abinda yayi mahaifiyarsa shi yayi tawa, zan iya cewa ma abu ɗaya ne amma Allah ya maidasu biyu, ina kaunar su sosai, kuma ina ƙaunar Mummyna ma Domin ita ɗin uwa ce tagari bata taɓa yimin abinda zanji cewa ba ita ta haifeni ba, fashewa yayi da kuka "abu ɗaya ne zaitamin zafi a zuciyata shine sanadina mahaifitata ta bar duniya" Toshe mishi baki daddy yayi tare da cewa "kul! Kada kace haka SARFRAZ, kowa akwai tashi kaddarar a rayuwa" Kusan a Tare suma su mum sukace "safraz kada kayi saɓo mana, Allah ya fimu sontane shiyasa ya amshi abinshi, kuma abinda zaka dage dashi ayanzu shine yi mata addu'a. Aayaann kam har yanzu ya kasa magana domin be taɓa tunanin sarfraz yanada hankali haka ba, itama dai Nawaz sai sharar ƙwalla takeyi ta rufe fuskarta da hijabi, gashi duka nauyin Mutanen faloun takeji musamman Daddy da mummyn Aayaan dashi kanshi Aayaan ɗin. Ita kam Aseey rai ƙwal tunda sarfraz yace ya haƙura da Nawaz. A hankali Nawaz ta mike da niyyar komawa ɗaki donta gani ko hassu ta tashi, dady ne yace "Amarya Nawwarah dawo ki zauna muyi maganar tarewarku keda Muhammad Ayatullah.. Kasa motsi Nawaz tayi a inda take, Aseey ta mike ta zaunar da ita tana cewa "zauna mana Amarya" Daddy ne yayi murmushinsu na manya tare da cewa amma fa SARFRAZ ya kamata ace Ranar da yayanka zai tare kaima a ɗaura maka Aure sai ayi shagalin tare. "Daddy Ni banida wadda nakeso fa" "Ina Yar fulaninka take? Ko itama baka sonta" Daddy yace yana kallon SARFRAZ. "Daddy nifa da..... Aseey ce ta hanashi karasa Maganar dayayi niyyah "wallahi daddy ka kawo shawara mekyau, domin yadda yarinyar nan tasha wahala dashi idan be auretaba be yi mata halalci ba. Girgiza kai kawai SARFRAZ yake yana murmushi "to ina take?" Sarfraz ɗin ya tambaya Da sauri Nawaz ta Miƙe "bari na kira ta" Bata jira amsar kowaba ta tafi da sauri saurinta Don bata son a tsaida ita domin zaman faloun ya isheta. Tana shiga ɗakin ta tarar da hassu zaune ta zabga uban tagumi. Ƙarasawa kusa da ita tayi "hassu lafiya naganki haka? Meyafaru? Ƙwal ƙwal hassu tayi da ido kaman zatayi kuka "Aunty dana tashi naga babu kowa duk sai tsoro ya kamani na zata kuntafi kun barnine" Murmushi Nawaz tayi "Lallai hassu ta dace da sarfraz halinsu kusan daya, "to yanzu kiyi hakuri, babu inda zamu tafi mu barki, muna babban falourne an haɗu ana magana, Yanzu hakama ke ake kira. "Muje in nuna Miki hanya" Nawaz tace Tare da kama kafaɗar hassu tana mikar da ita. Fita sukayi daga dakin, Nawaz ta nuna mata inda zatabi sannan ita kuma ta koma ɗaki. Hassu na zuwa falourn saita daburce ganin idon kowa akanta, rasa Wanda zata gaisar tayi sai kawai tace "barkanku da safiya". Gabanta sarfraz ya ƙarasa Tare da cewa "ikraam kina so na? Zaki aureni? Abinka da yarinta sai kawai hassu tahau murmushi Tare Da daga kai alamun eh sannan kuma ta furta da baki "Eh ina sonka, Wallahi zan aureka!" Batare data ji kunyar su Mummy da dady Dake zaune a falourn ba. Daddyn ne yace "yauwa Hafsatu, zo nan mu tattauna. Kunya rufe Mummy tayi, ai kuwa ta mike da sauri tayi hanyar dakinsu, itakam aseey sai murmushi take yi, tasan akwai sauran hassu, yarinta na cinta a ciki. Mummyn AAYAAN ma taji daɗin yadda SARFRAZ ya samu me sonshi bilhaƙƙi, har Saida tayiwa Aayaann addu'a a zuciyarta akan Allah yasa Nawaz tasoshi kamar haka. Aayaann duk ya ƙagu dayaga Nawaz Gashi yanajin Kunyar ya tashi daga faloun. Message ya turawa haidar "haidar don Allah ɗan kirani yanzu" Aiko cikin mintuna biyu wayar Aayaann ta hau ƙara, koda ya kalli screen ɗin sai yaga sunan haidar ɓaro ɓaro. Mummy ya kalla da dad "bari na amsa waya, colonel ne ya kirani. "Okay to jeka mana" Daddy yace tare da maida hankalinshi kan hassu yadda taketa murmushi, shi kanshi daddyn yasan hassu batasan meye aureba shiyasa taketa wannan fara'ar. Aayaann na fita daga faloun ya kashe wayar Tare da sakata a cikin aljihu. Direct ɗakin da Nawaz take ciki ya nufa, a zaune yaganta a Saman gado tana danna waya kuma ga dukkan alamu hankalinta yayi nisa da danna wayar, maida kofar yayi ya rufe ya samata key tare da takawa zuwa cikin ɗakin. Sai sannan Nawaz ta dago da kanta don ganin waye, Zaro Ido tayi ganin Aayaan yana smirking. Ruɗewa tayi ta rasa inda zatabi, shikuma ya fara murmushi gashi ya kafeta da ido "wa na kama? Ai duk gujegujen naki yaudai gani gaki" Fincikota yayi ta faɗo jikinshi, a tare suka sauke ajiyar zuciya, sosai ya rungumeta yanajin kamar ya maida ta ciki "sweetheart meyasa kike guduna? Meyasa bakya sona? Wallahi ni ina ƙaunarki kuma na tabbata cewa kece rayuwata, kinrigada kin saka min dafin sonki a cikin zuciyata kuma ya rigada yabi jini da tsoka ya taɓa ko ina. Ita dai Nawaz shiru tayi tana sauraren kalaman Aayann, tsayuwar ce yaji tana Neman gagararsa domin shi kaɗai yasan Yadda yakeji game da Nawaz, yana sonta yadda shi kanshi ba zai iya misaltawa ba, ji yake Kamar ya cinyeta ya huta. Saman gadon ya faɗa tana rungume a kirjinshi, sosai yakeson kasancewa da ita amma bayason ya bata mata rai "kin tuna sanda ina Eritrea nace ki shirya ranar dana dawo zamu Angwance? Sunne kanta tayi sosai a ƙirjinshi domin wata irin kunyar shice ta kamata. "To jiya dai na daga miki kafa amma yau kam Dole saina cire wannan kunyar dake wahalar Dani" Sosai Nawaz ta ruƙunƙumeshi kamar zata fasa ƙirjinshi ta shige, shikuma hakan da takeyi ba ƙaramin daɗi yakejiba. Fuskarta ya ɗago Wadda Idonta yake a rufe ruf, pink ɗin laɓɓanta ya zubawa Ido wanda daka kalleshi kasan zaiyi taushi duba da yadda yake ƙyalli Kamar ta shafa lip gloss. Sosai yaji gaba ɗaya tsigar jikinshi ta tashi yana neman rasa nutsuwarshi, samun kanshi yayi da hade bakin da nashi yana aika mata da wani irin zazzafan kiss Wanda shi kanshi besan ya iya ba, itakam Nawaz ta kasa tabuka komai kuma batayi yunƙurin kwace kanta ba illah zuciyarta da taketa bugawa da sauri da sauri. A haka a haka notinan kan Aayaan suka Fara kwancewa dominshi yana matuƙar son kiss arayuwarshi, fara bin sassan jikinta yayi da hannunshi yana yi mata tafiyar tsutsa. Da sauri Nawaz ta saki wata wawuyar ajiyar zuciya tare da riƙe hannunshi, gashi Babu damar magana bakinsu na haɗe Guri guda. Hannuwanta duka biyun ya haɗe ya riƙe da hannunshi guda ɗaya, ɗaya hannun kuma ya nufi kirjinta dashi. Saida ta sauke wani irin numfashi me ɗumi Jin tafikan Aayann saman kirjinta mararatan, motsi takeso tayi amma ta kasa kasan cewar ya sakar mata nauyinshi. Tanaji ya Fara wasa da albarkatun kirjinta yana numfashi da sauri da sauri, sosai tsoro ya kama Nawaz Ganin komai bada wasa yakeyiba, kuma a yanda ya kwance mata yanzu tasan me rabasu sai Allah. Firgicin be gama kama taba saida taji saukar ɗaya hannunshi a saman mararta yana ƙoƙarin chusa hannunshi cikin pant ɗinta. Zaro idanunta tayi waje tare dasa hannayen daya sakin mata tana dukanshi a baya.. Amma ko a jikinshi wai an yakushi kakkausa. Ƙoƙari take na kwace bakinta a nashi amma ta kasa, gashi gaba ɗaya yabi duk Wata gaba ta jikinta ya kasheta da ɗumin tafikan hannunshi, shi kanshi ya kasa control ɗin kanshi burin shi kawai ya samu nutsuwa. Sosai zuciyar Nawaz ta karye tana data sanin tasowarta daga faloun "yanzu idan yayi mata wani abu tasan kowa saiya gane, itakam idan hakan ta kasance batasan inda zatasa kanta ba saboda kunya. Numfashinta ne ya nemi ya ɗauke jin Aayaan na ƙokarin shiga tsakanin ƙafafunta. Ayimin afuwa kwana biyu kunjini shiru, jikinne har yanzu sai a hankali. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *59* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Zuciyarta kamar ta fashe saboda tsoro, gashi babu damar yin ihu tunda har yanzu bakinsu a haɗe yake. Zaro ido tayi sosai Yadda taji tudun length Dinshi na taɓa mata saman mara tasan idan ya chafketa ba ƙaramar wahala zata sha ba. Ji tayi kamar an sakata a Aljannah jin ana buga ƙofar ɗakin. Chak Aayaan ya tsaya da Abinda yakeyi, be ɗaga taba Saida aƙalla aka buga ƙofar ɗakin sau Kusan Biyar Sannan ya dagata yana cewa "Allah ya Taimakemu dukanmu, amma da yau hmmm, jeki buɗe kofar" cikin wata irin kasalalliyar murya Rimi-rimi Nawaz ta tashi daga gadon kamar zata buɗe ƙofar, ai kuwa ta faki idonshi ta afka bayi da gudu tare da zira jamlock. Murmushi yayi Tare Da girgiza kai Sannan ya miƙe ya nufi kofar, saida ya tsaya ya ɗan gyara zaman rigarshi tare da barbaza gashin kanshi Sannan ya buɗe kofar. Aseey ce tsaye da gani ta ƙagu da'a buɗe mata kofar, kallon Farko data yi mishi ta gane ba ƙalau ba (kundai san Aseey tayi degree a wajen sa ido). Cikin ɗakin take kallo "ina sister Nawaz ɗin? "Tana bathroom" Aayaan yace Tare Da bata hanya tana shiga cikin ɗakin, shima bayanta yabi ya koma ya zauna a bakin gado. Murya Aseey ta ɗaga tare da cewa "sister yi sauri ki fito Akwai labari mai zafi banso ya huce. Kallon Aayaan takeyi tanason tayi dariya amma bataso ya ɗauki wani abu a ranshi, a zuciyarta take zancen zuci "A to aikai ka sani, adaiyi mugani idan tusa zata hura wuta! tunda ka zauna wai kai mai mata, bakaso ta wahala, aikai kuma kayanki ticket ɗin wahala, abinda da anyi so ɗaya an Wuce gun amma har yanzu fama akeyi wai kai me tausayi, zan dai ga ƙarshen wannan tausayin" Saida murmushi yayi nasarar suɓuce mata. Ɗage gira Aayaan yayi "lafiya dai kike dariya ke kaɗai? Ɗan daburdabur tayi sannan tace "wallahi shirmen hassu da sarfraz ne yake bani dariya" Kafaɗa ya ɗage alamun ko oho, "nifa Banga lefin suba. Domin dole ne na nunawa wanda nakeso inasonshi, babu wani shirme" Nawaz dake cikin bayi Saida taji dama ƙasa ta tsage ta rufta ciki jin Muryar Aseey datayi, tasanta dasa ido ga bin ƙwaƙwƙwafin tsiya. Kunna pampo tayi ta wanke fuskarta, sannan ta duƙa don tayi fitsari sai taji pant ɗinta a jiƙe, tsaki tayi "Mtsewwwss" don tasan ko menene koda bata duba ba. "Wai meyasa zuciya take hakane? Duk irin firgicin danake ciki saida tasa jikina yayi reacting." Gama gyara jikinta tayi sannan ta ɗauki towel ta goge fuskarta. Cikin sanɗa ta buɗe ƙofar, aikam karaf suka haɗa Ido da Aseey, ɗan murmushi Aseey tayi don Yadda taga idon Nawaz yayi wuri-wuri ga laɓɓanta sunyi wani irin pink, ko ba'a faɗa mataba tasan ƙaninta ya rage zafi. "Sister yi sauri ki ƙaraso mana! Kada fa Labarin ya huce! Ɗan ƙara karsashin jikinta tayi tare da ƙarasawa kusa da Aseey ɗin tana zama. Sosai Aayaann ya dage yanaso su haɗa ido amma fir Nawaz taki yarda, duka ta maida hankalinta kan Aseey, amma Wata Irin kunya na lullube da ita, don Babu yadda zatayi ne shiyasa kawai na danne ta fito. "Mummy ce tace zamu tafi sudan wajen yan uwanta nachan, kuma daganan zamuje gidan Aunty khatoume tayi mana gyaran jiki na sati ɗaya, Amma kafin nan sai mun fara komawa maiduguri saboda kije kiga ƴan uwa. Kuma wai za'a tafi da Daddy harda mummy da Sarfraz ma, au harda su hassu fa, koma ince duka zamu tafi saboda wai za'a je a nemawa Sarfraz auren hassu kuma shima SARFRAZ ɗin zaije danginshi, and mummy ma tace tanaso kije dangin dad ɗinmu su ganki saboda suma basu sanki ba. Aayaann ne yace "haba sis ji yanda kiketa haɗa magana guri ɗaya, ai ba lallai ta fahimci me kike son faɗa mata ba. "To mai mata, ai sai ka koyamin yadda ake magana, Nidai yanzu zan fara shiri saboda gobe da wuri zamu ɗauki hanya, kuma bari kaji, a Maiduguri zamu barku kaida SARFRAZ domin baza ku bimu sudan ɗinba nasanku da rashin ta Ido, nida hassu da sister Nawaz da Mummy kawai zamu tafi. Ku kuma saiku zauna achan Maiduguri, idan kuma zaku biyo su Mummy da Daddy ku dawo Zarian ne ku kuka sani. "Naji" abinda Aayaan yace kenan, don duk haushi ya kamashi, wai sudan? Shidai har yanzu baza'a bar mishi mata ta huta ba kenan. Miƙewa Aseey tayi "bari naje gurin mummy naji yadda za'a gama maganar" sannan ta nufi hanyar fita, itama Nawaz sai tayi wuf tabi bayanta don bazata yarda Aayaan yaja mata abin kunya ba, don ta lura da gaske yake yi. Aseey na fita ya fincikota tayo baya, ihu zata zabga yayi saurin sa hannu ya toshe mata baki "ina zakije bayan kin gama tara min wahala a marata? Dole ki san Yadda za'ayi in samu relief don wallahi bazan yarda inyi ciwon cikiba bayan gaki. Runtse ido Nawaz tayi domin maganganun shi sunyi mata nauyi a zuciya, tanaji yana yadda yaga dama da jikinta amma Babu damar hanawa, burinta ya samu relief ɗin ya rabu da ita, kada ta hana shi yayi mata me gaba ɗaya. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Tun Ranar da su umma suka dawo daga gurin boka kafar umma taketa hauhawa, ta kumbura tayi suntum sai ƙyalli takeyi ga wani ruwa da take zubarwa. "Umma ya kamata fa muje asibiti a duba kafar nan saboda abinfa ya fara bani tsoro, domin ji Yadda nan gurin yayi kamar ya ruɓe! Nifa tsorona ɗaya kada ace cancer ce a ƙafar nan. "Fauziyya Ni kaɗai nasan abinda nakeji a kafar nan, wallahi har tsoron zuwa Asibitin nakeyi kada a faɗa min abinda zuciyata bazata iya ɗauka ba. "Kuma abu na biyu daya dameni shine sam jamila taƙi dawowa gida, Gashi ko kiranta nayi bata ɗaukar wayar. Fauziyya ce tace "Umma tun farko ke kika sakin mata, wani zubin fa har cewa kikeyi basai ta dawo Hutu ba tayi zamanta achan, to yanzu Kinga abin ya fara damunki. Gaba ɗaya umma tayi laushi, ga alamun nadama nan ƙarara a Tare Da ita Saidai bata furta hakan ba. "Fauziyya nina san halin danake ciki a yanzu, gaba ɗaya duniyar tayi min zafi, nama rasa me zanyi inji sanyi a zuciya ta. "Umma Ni a tunani na ya kamata ki cire wannan kishin da neman fansan haka a cikin zuciyar ki, saboda dalilin hakan nefa kika samu ciwon ƙafar nan, gashi Yanzu ko takawa bakya iyayi. "Fauziyya aini tuni na saduda, babu Ni babu kuma zuwa gurin boka ko wane iri ne, abinda zaki duba shine Ni danake zuwa gurin bokan nice kullum cikin walaha da kashe kuɗi, idan kin lura su ko a jikinsu gashi sam babu wani abu dayake samunsu koda bokan yace zai samesu. "Nima dai haka nagani umma, kullum mune kaiwa boka kuɗi, Mu kuma muna nan muna nema, Ni kaina yanzu sale duk ya chanza min, umman shima ko kallona batayi. Ɗan gicciyawa umma tayi domin gaba ɗaya ta gaji da zama guri ɗaya, gashi kuma ba iya tashi zatayi ba domin ko motsa ƙafar tayi wata irin azaba ce ke ziyartar ƙwaƙwalwarta, a zuciyarta sai tsinewa bokan takeyi. "Fauziyya yaushe zakije Makarantar su Jamila ki dubo min wane hali take ciki?" "Umma gaskiya a halin da kike ciki bazan iya tafiya wani guri na bar ki ke kaɗai ba" "Fauziyya don Allah badon niba ki taimaka kije ki gano min meke faruwa wallahi tun shekaranjiya take fado min a zuciya, kuma kinsan ko dama Jamila ba Wani jin magana takeyiba" "To umma zanje! Amma saina samo wanda zai kula dake kafin na dawo" "To fauziyya Nagode" Duk sai fauziyya taji tausayin umma ya kamata sosai, duk jikinta yayi sanyi tama rasa me zatayi, yanzu haka tana nadamar abubuwan da suka aikata akan Nawaz. "To yanzu haka ma ina Nawaz ɗin take? Ina ummi? A Wane hali sukema? Fauziyya ke zancen zuci (Nikam matar Rasheed nace suna hali me kyau domin hassada game rabo taki ce) °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Da kyar Nawaz ta kwaci kanta a gurin Aayaan shima don hassu ta shigo dakin ne, koda ya fita dakin SARFRAZ ya koma Tare da kiran securities ɗinshi a waya yana shaida musu Cewa su shirya gobe da sassafe zasu tafi Maiduguri, Sannan ya tashi ya shiga bathroom don tsaftace jikinshi. Sarfraz da bandi kuwa mota suka ɗauka suka nausa cikin gari don zagayawa wajen abokan Sarfraz ɗin, domin susan ya dawo, har HAYATUL ISLAM sukeda niyar zuwa. Nawaz na kwance ne amma tunani ya cika mata zuciya, tsoron yadda zata ƙare da Aayaan takeyi duk randa hakurinshi ya kare, domin ta lura hakurinshi Ya kusa karewa daurewa kawai yakeyi, kuma a jarabar mazan yanzu ma Aishi sai dai a bashi girma don kuwa ya nuna shi mai dattako ne. Abu ɗaya ne yaƙe sanyaya mata zuciya shine gobe zataje taga umminta, ta kwanta a jikinta taji duminta kuma su tattauna abubuwa da dama wanda da bata samu damar faɗa mata ba. Hassu kam murna takeyi bilhaƙƙi saboda zata auri SARFRAZ, bini bini sai tayi murmushi har ɗan tsalle takeyi, ita dai Nawaz sai dai ta kalleta ta kauda kai, domin tasan kuruciya ke damun ta, domin data San me zata tarar bazatayi wannan murnar ba, kuma ta lura shima SARFRAZ ɗin ba baya bane wajen jaraba domin ba zai ɗaga mata kafa Kamar Yadda Aayaan yayi ba. °°°°°° Washe gari Misalin ƙarfe Bakwai na safe su mummy da mumyn Aayaan da dai sauran duka Yan gidan harda Daddy aka ɗauki hanyar Maiduguri. Tsaf Aayaan ya cire kunya yace shi mota ɗaya yakeso Shida matarshi, Mummy da mummyn sarfraz da Aseey da muhsien suma mota ɗaya, hassu da sarfraz da bandi da Daddy suma mota ɗaya. Nawaz kam ba haka tasoba taso a basu ɗaya ne ita da Aseey da hassu amma Aayaann yayi ruwa yayi tsaki ya shafe idonshi da toka yace basan zancen ba. Tunda suka shiga motar yake lalubeta, daga ya taɓa nan saiya taɓa chan, tayi tayi ya bari amma kamar ma ƙara zugashi takeyi, daga ƙarshe ma banza tayi dashi sai dai intaga zai wuce gona da iri tace "bafa mu kaɗai bane akwai driver" shine zai ɗan sassauta mata. A azare suka tsaya sukayi Sallah sannan suka kuma ɗaukar hanya, sosai tafiyar tasu take sauri domin a jere suke tafiya kuma hanyar babu cunkoso, sanda suka iso dai dai gurin da Yan ta'adda suka tsaresu saida Nawaz taji firgici ya kamata amma ganin an wuce salin alin yasa taji zuciyarta tayi sanyi. Duk abinda take yi Aayaann na lura da ita, barcine fal idonta amma taki yarda tayi saboda kada Aayann ya rungume ta, amma saida yaci karfinta tayishi bata shiryaba. Sai yammah lis suka isa maiduguri, domin har an fara kiraye kiyaren magrib. A gidan su Aayaann aka yada Zango domin kowa ya huta gajiya. Oga Aayaann kuma sai haɗa Target yake na yadda Nawaz zata kwana a dakinshi.... Ina yiwa kofa fatan Alkhairi, *SISTER NAJIDAT BICHI WANNAN SHAFIN NAKINE* *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *60* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Wannan shafin nakine *KHADIJAT SUNUSI LAWAL (SEEMAH)* Kiyi yadda kikaga dama dashi domin nakike halak malak "Aayaan yace a baki shi kyauta" Haƙarshi bata cimma ruwaba domin tunda ta shiga ɗaki taƙi fitowa, Sannan kuma daya dameta da kira a waya ta kashe wayar. Duk Aseey na ankare da abinda ke faruwa sai dai tayi murmushi tace "kaɗan ka gani, har dai aka cemaka mace ai an gama komai." Washegari gidansu ummin Nawaz aka fara zuwa, kowa sai mamakin Yadda Nawaz ta cika yake, wasuma gani sukeyi kila ciki gareta. Baffa ma ba ƙaramin daɗi yajiba yadda yaga Nawaz ɗin yasan In'sha Allah sun rigada sun haɗa kansu ba sai ya tsaya dogon jawabi ba. Ummi kuwa kamar ta cinye Nawaz ɗin tsabar murna, tama rasa inda zatasa ta. Su mummyn Aayaan da Mummyn SARFRAZ sun samu tarba me kyau sosai, haka ma dady shima sai mamakin irin karamcin su yakeyi, don tunda suka sauka a gidan kowa sai haba-haba yakeyi dasu, cikin ƙanƙanin lokaci aka dama musu fura taji mai da kwakwa, ga farfesun zabi da burabusko sai kamshi yakeyi. SARFRAZ da bandi cikin gari suka bazama don ba idanuwansu abinci, shi kuma Aayaan yana fada shida baffa domin yayi duk yadda zaiyi yaga Nawaz Amma abu yaci tura, Mummyn SARFRAZ da Mummyn Aayaan kuma kwantawa sukayi don su miƙe jiki su samu relief ɗin zaman da sukayi na mota. Aseey da Nawaz da hassu kuma suna ɗakin kaka sunata hira dasu ummi, muhsien na fara rigima ummi ta ɗauke shi ta goya, Aseey sai dariya takeyi tana cewa "mama don Allah ki sauke wannan gardin kada ya gajiyar dake" Ummi kam tace ta kyalesu babu ruwanta, haka dai aka yini kowa cikin farinciki da walwala. Kwana ɗaya sukayi suka ɗauki hanyar rigar su bandi Domin aje gurin malam aji yadda za'a nemi auren hassu, sanda zasu tafi saida kowa yaji babu daɗi a gidan kakannin Nawaz. hakanan dai aka rabu badon zuciya nasoba. Cikin ikon Allah koda suka isa rugar sai suka tarar iyayensu hassu ɗin sun dawo daga yawon kiwon jiya, malam ma yana gidan domin yazo yayi musu bayanin abubuwan da suka faru bayan basa nan. Murna gurin Bandi ba'a magana domin da gudu yaje ya dire a jikin ummansu, itama hassu haka domin mancewa dasu Sarfraz tayi ta fara taɓararta son rai. Bayan komai ya lafa ne Daddy yayi bayanin Abinda ya kawo su, wato sunaso abasu auren hassu inda hali, kuma sunaso ne ayi bikin cikin ƙanƙanin Lokaci. Basu wani nuna wata damuwa ba, domin mutanene masu karamci da girmama baƙi, dukda dai daka kallesu zakasan fulanin daji ne amma sunada faran faran da mutane, farinciki a gurin malam ba'a magana tunda ya gama jin abinda ya kawosu dady yaketa kabbara "Allahu Akbar, Ashe hassu mijine ya biyota har gida, Allah dai ya tabbatar mana da Alkhairi" "Ameen" kowa yace Daddy ne ya Nemi alfarmar cewa don Allah su dena tafiya kiwon da suke zuwa, su zauna a gida za'a samu wanda za'a ba ya riƙa zuwan musu kiwon, sannan za'a chanza musu gida a fitar dasu cikin gari dasu da baffa malam. Ansha gwagwarmaya kafin su yarda amma daga baya sukace sun amince. Gyaran murya Aayaan yayi Sannan yace "Daddy idan babu matsala inason na ɗauki nauyin gidajen da zasu zauna, yanzu zanyi waya nasa a nemar musu masu kyau a cikin gari. "Aayaann baka gajiya da hidima, babu Komai Allah ya bada lada kuma yasa ka gama da duniya lafiya, yabaka masu yi maka fin wanda kayi wa jama'a. Kowa saida ya amsa da "Ameen" Wata alfarmar suka kuma nema "sunaso su koma da hassu da bandi, domin za'a fara shirye shiryen bikin, kuma bandi anason a nemi makaranta mekyau asashi yaci gaba, Aayaan ne ya bada sadakin hassu dubu ɗari biyu cif. Sannan sukayi haramar tafiya da Alkawarin idan bikin yakusa da kwana uku zasu aiko da mota ta kwashesu duka zuwa Zaria ɗin, don sun nemi alfarmar ayi duka taron bikin achan. Daganan gidansu daddyn Aayaan aka wuce dayake Babu nisa sosai tsakani. Sosai sukayi farinciki suma, kuma dama duk sun ƙagu suga amaryar Aayaan ɗin, sai Sannan ma mummy ta tuna da Ashley dataga kannenta, zancen zuci ta fara "to ina Ashley ɗin take? Bata gida dai sanda muka sauka, Sannan namma da alamun batanan, kawar da zancen kawai tayi daga zuciyarta don bata son damuwa. Gabatar musu da Sarfraz tayi tareda Daddy da mummy, sosai sukayi mata barka domin suma sunsan labarin biyuninta mumtaz. Flat guda aka basu akace su zauna, kowa sai nan nan yakeyi da Nawaz. Domin sun lura akwaita da kunya ga hankali. Kwana biyu sukayi anan saboda akwai gidajen da aka ɗan zazzaga na dangi. Kakan Aayaan shima yaji daɗin Kasancewar Nawaz a matsayin matar jikanshi, dayake duk baffa "(kakan Nawaz na Wajen uwa) yayi mishi bayani tun tuni, kuma ƙarin farincikin shi shine itadin jinin amininsa ce. Daga nan gidan kakannin nawaz na ɓangaren babanta suka wuce, basuso su kwana ba amma fir suka dage akan sai sun kwana, kundai san Mutanen da akwai son baƙi. Cikin dare kakar Nawaz wadda akasa mata sunanta (Nawwarah) ta tashi Nawaz tare da bata Wani rubutu data zuba zuma da garin kanumfari aciki tace ta shanye, da sassafe ma suna tashi ta bata wani tace ta shanye.. Sosai kaka malam yaketa nan nan da sarfraz da Aayaan, domin lokaci ɗaya yaji sun shigar mishi zuciya Ko Bayan sun gama shiryawa da nufin tafiya Saida kaka taja Nawaz gefe ta ƙara bata wani haɗin tace ta shanye. A gajiye suka koma gida, don haka babu wanda yabi takan abinci, kowa makwanci ya nema ya miƙe jikinshi tunda dama basu baro chan gidanba saida sukayi dam. Koda gari ya waye babu wanda ya fito falour domin kowa yananan kwance sai juyi yakeyi, shikuma dady tun bayan asuba yacewa mummyn zai fita Saboda yanason yaje Wajen abokanshi nanan Maidugurin. Ganin yadda kowa ke malelekuwa a gado yasa Nawaz ta tashi ta shiga kitchen domin tasan Aseey ba tashi zatayi ta dafa abinci ba, kuma ai da kunya ace gasu amma a bari har sai su Mummy sun shiga kitchen sun dafa abinci. Tana cikin gyara kayan miya taji kamar motsin mutum a bayanta, ai kuwa tana juyawa sukayi ido huɗu da Aayaan. Wata ƙayatacciyar dariya yayi mai kama da murmushi sannan ya nufi inda Nawaz ɗin take tsaye, kama kwankwasonta yayi ya haɗa da nashi Sannan yasa ɗaya hannun yana ɗago da fuskarta sama don su kalli juna dakyau "wa na kama? Wato Ni kike gudun mawa ko? Har waya kika kashe saboda kada na kira ki Koh? "To yanzu wa na kama?" Duk yadda Nawaz ɗin ta fara sabawa da Aayaan amma hakan be hana zuciyarta bugawa sosai ba, ga jikinta sai amsawa yakeyi, bata iya buɗe baki tace mishi komai ba illa ma Idonta data rufe. Tsintar bakinshi tayi cikin nata, saida yayi mata kiss kamar na Three minute Sannan ya cire bakinshi tare da Cewa "morning kiss" Ita dai Nawaz har yanzu batace uffan ba Domin ta gama saduda da cewa shi ɗin mijinta ne kuma akwai manya manyan haƙƙoƙinshi akanta. "Look! Kiyi min magana mana! Nifa nafison Nawaz mara kunya ba Nawaz me shiru shiru ba, nafison me murguɗa min baki da mai hararata ba wadda zatayi shiru tana kallona ba. Ko yanzun ma dai batace komai ba, sakinta yayi yana murmushi Sannan ya nufi mugsrack don ɗauko mug ya haɗa tea, ai kuwa da gudu ta arta tare da cewa, "ai Wannan Nawaz ɗin ta wuce mai murguda baki me Mari da mazurai ce, inta kama ma harda duka" Waigowa Aayaan yayi baki buɗe yana mamakin wai Nawaz dince da gaske "eh Lallai! Wallahi zamu haɗu ne sai kin min bayani dalla-dalla. Harara taketa balla mishi harta shige ɗaki, shidai Aayaan dalau yayi yana mamakin wai Nawaz dince haka? "Lallai ne yarinya! zan kamaki a hannu? Girkin da Nawaz batayiba kenan, sai karyar ciwonkai da tayiwa Aseey. Kwanansu biyu da komawa gidansu Aayaan, zuwa lokacin kowa ya huce gajiya. Aayaann Mummy ta kira tasashi yayi musu passport da visa don tafiya sudan, ita kuma mummyn SARFRAZ da daddy sukayi haramar komawa zaria saboda su fara haramar shirye shiryen biki. Shikam SARFRAZ cewa yayi zai zauna shida Aayaan anan Maidugurin, idan Aayaan ɗin ya gama abinda yake yi zasu koma Zaria ɗin tare, haka shima Bandi yace yaga gurin zama tunda dama shine aminin SARFRAZ ɗin Ayanzu. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sun sauka lafiya, inda suka sauka a gidan iyayen riƙon Mummy, sosai sukaji daɗi, rasa inda zasu sasu sukayi tsabar murna. Har wata kula ta musamman akeba Nawaz jin ance ita ɗin matar Aayaan ce. Kwanansu biyu anan mummy ta kaisu gidan aunty khatoume, sosai tayi mata bayanin yadda takeso gyaran jikin nasu ya kasance. Inda takeso ayiwa hassu na cicciko da jiki da gyaran fata, ita dama Nawaz bai wuce na gyaran fata da Ni'ima. Madam Aseey kuma me gaba ɗaya ne, gyaran jiki da Ni'ima da matsi. Sosai khatoume ta bada himma don gyara su, inda a ranar farko tunda asuba ta tashi ta cika wasu manyan bawuna guda uku da ruwan turare tare da zuba musu wani haɗi na musamman. Saida yakai minti goma da haɗawa lokacin ya rage zafi Sannan tace kowa ya shiga cikin bawo ɗaya ya zauna, Kasancewar bawon Babba ne sosai sai ya zamana duka jikinsu na ciki illah kansu ne kaɗai a waje. Sunfi minti talatin da shiga ciki amma babu alamun Aunty khatoume zatace su fito, hatta Aseey dake ɗokin gyaran saida ta fara gajiya. Saida aƙalla sukayi awa ɗaya da shiga Sannan tace su fito. Nanma ɗaurin kirji tasa sukayi Sannan ta dauko wani abu kamar tunkuza ta fara murza musu ajiki, duk inda ta murza sai yayi wani irin taushi da santsi da haske kamar Fatar jariri dayake fatar ta riga ta jiku a ruwan da suka shiga. Duk wunin ranar a wahale suka yishi, sai yamma liss Sannan suka samu damar hutawa, nanma dai magunguna ne iri iri take kawo musu a kofi tace su shanye su bata kofin. A kwana biyu sunyi kamar basuba, hassu kam har ƙirji ya fara Cikowa kamar na cikakkiyar budurwa. Aseey ce ta lura Kamar idan aka kawo magani Nawaz batasha, bayi take shiga ta juye. Zuwa tayi ta samu Aunty khatoume tayi mata bayanin Abinda Nawaz ɗin keyi "Amma Aseey ba mummy tace matar Aayaan bace?" Cewar Aunty khatoume tana kallon Aseey. "Eh matar shice amma basu tareba" "No wonder! Nasan tsoron gamonsu takeyi shiyasa bata sha, amma kibarni da ita zanyi mata dabara. Sosai Aseey taji daɗi domin tasan Aunty khatoume akwai aiki da cikawa. Sai washegari Nawaz na zaune bayan ta idar da sallah, su hassu da Aseey suna Babban falourn Aunty khatoume suna kallo. Sallama Aunty khatoume tayi ta zauna a gefen Nawaz "ƴata kina Lafiya? Murmushi Nawaz tayi tace lafiya lau Aunty kaina ne kawai yakemin ciwo" "Ayyah sannu kinji" "Yauwa Aunty Nagode" Nawaz tace tana daɗa yin murmushi. "In bazaki damuba inaso muyi wata magana dake, amma kafin nan inaso ki kalleni a matsayin uwa ko yaya. Murmushi Nawaz tayi tace "babu komai aunty inaji" "Kuntaɓa samun kusancin juna keda mijinki?" Tambayar tazo ma Nawaz a bazata amma saita tuna maganarsu ta farko, kirgiza kai Nawaz tayi alamun a'a. "Yauwa to, Nagode da bakiyimin karya ba, dama ina so na taimaka miki ne, akwai maganin dazan baki hardai kika juri shanshi to In'sha Allah koda anzo wajen kwanciya bazakisha wahala ba domin zaisa jikinki ya buɗe ne. Ɗan murmushi Nawaz tayi "Aunty da gaske? Murmushin manya khatoume tayi ganin ta samu amsar zargin datakeyi cikin sauƙi. Dafa kafaɗar Nawaz tayi "dagaske ƴata amma ina so kada ki faɗawa kowa munyi wannan Maganar dake. "To aunty amma don Allah itama hassu abata wallahi tausayinta nakeji gashi SARFRAZ ba wani hakanli bane ya isheshi. To daughter kada ki damu itama zan riƙa bata, amma burina ki riƙe mana sirri koda wasa kada ki faɗawa kowa. "To Aunty bazan faɗawa kowaba, nayi alkawari... Nawaz tace Tare Da jin wani daɗi a cikin zuciyarta.. Ita kuma khatoume ta tashi ta Wuce daki. Tundaga ranar idan aka Kawo magani saita riga kowa shanyewa, wani zubin har kakkaɓe kofin takeyi. (Nidai Nace Nawaz babu girma saina shekaru, kedai babu wuya ayi miki wayau) Yanzu zamuji ya haduwar hassu da Sarfraz zata kaya, da kuma Oga Aayaan da madam Nawaz. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *61* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* _*Sister SAFIYYAH HASSAN (UMMEE) Tsakanin keda A.M INUWA Bansan wayafi ƙaunar Sarfraz ba! Saboda haka bansan wa zan ba kyautar wannan page ɗin ba acikin ku biyun, kawai kuyi hakuri ku raba 50 50 😎*_ Aseey kam duk abinda Nawaz ɗin take yi tana sane da ita, sai dai tayita dariya a fakaice tana ganin wautar Nawaz ɗin a fili, wato so takeyi jikinta ya buɗe shiyasa taketa faman bankar magani, Batasan akasin haka bane zai faru. A maimakon gyaran sati ɗaya sai mummy tace kawai ayi musu na kwana goma, kenan an ƙara kwana uku akai. Sosai suka chanza kamar basuba musamman hassu da ada take Ƴar mitsitsiya, ita kanta Nawaz haka zata zauna tayita kallon kanta a mudubi, fatarta har wani milk milk takeyi ga wani taushi da santsi da tayi, kuma kullum cikin kamshi take koda bata shafa turare ba, abin har mamaki yake bata, wai itace ta zama haka. Ta ɓangaren hassu kuwa jiki ya gama buɗewa sosai domin ta zama wata uwar mata duk wani shape ɗin dazai nuna ita macece ya fito fili, kayan ma da akazo mata dasu tuni sunyi mata kaɗan. Ko sau ɗaya Aayaan be taɓa kiran kowaba, wai shi ala dole yayi fushi musamman da suka ƙara kwana ukun nan, itama mummy ganin be kiraba tasan me yake nufi shiyasa itama bata kirashiba ta shareshi kamar yadda ya sharesu tasan ya kusa shigowa hannu. Manya manyan kwalaye guda uku Aunty khatoume ta shirya musu kayayyakin su aciki, waɗanda suka kama dasu turaren wuta, humrah, dabulun Dilke, coleccher, zuma, Tsumi, garin magunguna, turaren tsuguno dadai sauransu. Sosai Mummy tayi mata godia ganin yadda yaran nata suka koma gwanin ban sha'awa, har kuɗi Mummyn ta ƙara mata akan wanda ta buƙata domin nuna jin daɗin ta. Komawa gidan su iyayen riƙon mummy sukayi gaba dayansu suka kwana ɗaya domin su gama shirye shiryen su. Sosai iyayen mummyn suke nuna farinciki, Saida suka tsaida cewa zasuzo Nigeria bayan su mummy sun koma da Wata uku, bayan sun gama haɗa komai ne Sannan sukayi haramar komawa gida Nigeria. Babu wanda Mummy ta faɗawa zasu dawo saidai saukar su aka gani kamar daga sama, saboda da suka sauka a Airport ɗin kano bata kira driver ba kawai saita samu mota tayi shata zuwa Zaria. Sosai Mummyn SARFRAZ taji daɗin dawowarsu domin an tsaida Ranar juma'a za'a ɗaura auren sarfraz da hassu Sannan a haɗa tarewar su data Nawaz da Aayaann, kuma mummyn Aayaan kashe watoyinta tayi sanda suka isa sudan ɗin, koda Mummyn SARFRAZ ɗin sau ɗaya suka taba yin waya. Duk Mummyn SARFRAZ ɗin ta shiga damuwa kada suƙi dawowa gashi an raba iv card ko ina. Shiyasa data gansu daɗi ya kamata kamar tayi mene don farinciki da murna, tsaye tayi tana kallon yadda su hassu suka koma, gani takeyi ma kamar ba hassun ba, sai Nawaz itama da gaba ɗaya ta chanza ta kara cikowa fiye da da. Ita Aseey ma ba'a magana Domin ita abun biyu ya haɗe mata da gyaran jikin da salo da salasalar da taketa yi. Godiya sosai mummyn sarfraz tayiwa Mummyn Aayaan Kamar zata ari baki, taji daɗin yadda taga hassu ɗin Takoma, domin dama kullum da tausayinta take kwana, tasan cewa idan SARFRAZ ya hake mata ba karamar wahala zatashaba tunda shi mabuƙaci ne, amma yanzu alamu sun nuna zata iya jurewa sai dai ɗan abinda ba'a rasa ba kafin ta saba sosai. Haikan ake shirye shiryen bikin saboda wasu daga cikin ƴan uwan Mummy da dadyn sarfraz har sun fara zuwa, saboda ya kama saura kwana huɗu biki. Sosai Daddy shima yayi ƙoƙarin aikawa kowa da iv card, wadanda kuma sukayi nisa da yawa ya kirasu a waya ya shaida musu. Har ranar babu SARFRAZ babu Aayaan babu bandi, kuma abin ya fara ba mummy tsoro kada fa suki zuwa Azo ayi biki babu ango domin ko basu zoba baza'a fasa ɗaurin auren ba. Washegari ya kama saura kwana uku biki, su mummy dasu Aunty Aseey duk suna zaune a falour suna hira tare da baƙin da suka fara zuwa. Harabar Gidanne ya cika da hayaniya tare da ƙarar motoci. Miƙewa Aseey tayi ta buɗe labulen window ta leƙa harabar gidan don ganin meke faruwa. Ai kuwa da sauri ta waigo tare da cewa mummy Wallahi Aayaann ne tare da su ummin Nawaz dasu umman hassu motoci ne da yawa kamar sun tawo da duka dangi. Tana kaiwa nan tayi waje da gudu itama Nawaz bata ko dauki mayafi ba ta arta a guje jin ance harda umminta, hassu ma ta take mata baya. Aseey na zuwa ta afka jikin Aayaann tana cewa "gaskiya my bro kaina musamman ne domin nasan wannan duka aikin kane" sakin baki da hanci Aayaan yayi yana kallon Nawaz wadda ta zundumo da gudu duka jikinta babu inda baya motsawa, ita kuma gaba ɗaya hankalinta yayi gaba bata kallon kowa in banda umminta, tana zuwa ta faɗa jikinta tana fashewa da kukan shagwaɓa. Aseey kuma jin Aayaan be bata amsa ba yasa ta ɗago kanta don Ganin meke faruwa, aikuwa taga duka hankalinshi ya tafi zuwa guri guda. Bin inda yake kallo tayi itama, sai kawai taga Ashe Nawaz yake kallo, kyalkyalewa tayi dariya tana tafi "hmm kaɗan ka gani, wallahi idan ka tsaya sanya wani zai kwace maka ita don naga alamun kamar rashin rabone yake bibiyarka. Duk wannan Maganar da aseey tayi sam Aayaan babu Wadda yaji aciki, idonshi nakan Nawaz yadda takeyiwa umminta shagwaba saiyaji duka notikan kanshi suna kwancewa yana neman manta inda yake. SARFRAZ ma ya tawo da sauri zai shiga gurin mummy ya faɗa mata sun dawo, wata yagani kamar hassu zata giftashi da gudu, sai dai ita wannan tafi hassu kyau da cika da komai, sakin baki yayi ya bita da kallo "lallai wai dama hassu nada yaya shine Ni za'a haɗani da wannan Yar mitsitsiyar? To wallahi da sake! Don bazan yarda inyi biyu babu ba, wato babu wan babu ƙanin, na rasa Nawaz Sannan a haɗani da waccar jaririyar dukda tanada gurbi na musamman a cikin zuciyata. Cikin falourn ya shiga yana girgiza kanshi alamun akwai rikici. Mummy da Mummyn Aayaan sukuma sunata faman buɗe sauran ɗakunan dasuke arufe saboda jama'ar sunyi yawa dole ne a nemar musu matsuguni me yalwa. SARFRAZ sai bin Mummy yakeyi yana cewa shifa yanada magana. Balla mishi harara Mummyn tayi tare da cewa "SARFRAZ don Allah ka rabu Dani baka ganin aiki nakeyi? Ka haɗiye duk abinda kakeson faɗa min zuwa anjima idan na samu lokaci saika faɗamin" Rokonta yakeyi domin shi gani yake kamar duk ƙarin second ɗaya kamar yana ƙara nisanta shi da yayar hassu daya ganine, (lols jama'ar SARFRAZ kunji rashin ta ido gun Sarfraz ko? Harda son banza da yayi mishi yawa, yaga yarinya ɓulɓul dumi dumi zai juyawa hassu baya) Ganin Mummyn ba kulashi zatayi ba yasa ya juya cikin fushi ya koma harabar gidan, dasu Nawaz yaci karo suma sun tawo ita da umminta da kaka zasu shiga faloun, Saida ya firgita yadda yaga Nawaz ɗin ta koma. Sai yaji ya ƙara samun kwarin guiwar kin Auren hassu ɗin, gaishe dasu ummin Nawaz ɗin yayi tare da raɓawa ta gefe ya wuce yana ƙarewa Nawaz kallo a fakaice "kut! Billahil azeem zabai yiwuba, jifa yadda Nawaz ta koma! Kenan Ni aka rainawa wayau da za'a haɗa da waccar ƴar ficikar." (Nidai Matar Rasheed nace kuji Sarfraz da jaraba🙃 wato yama manta cewa shiyace a aura mishi hassun don yaga mai full package 🫣🫣) Shidai Aayaan harya fara dana sanin kin kiransu sanda suna sudan, kuma yasan tunda mummy bata kirashiba itama tayi fushi, yanzu kenan akwai ƙura domin ba lallai ta yarda ta bashi Nawaz cikin sauƙi ba. Yana wannan tunanin saiga Sarfraz ya ƙaraso gurinshi yana ƙunci. Kallonshi Aayaan ɗin yayi Tare Da cewa "bro meya faru naga Kamar da matsala?" "Wallahi yaya akwai matsala babba ma, yanzu fisbilillah ni zanje inaso nayi magana da Mummy emergency amma fir taƙi saurarena, wai saita gama shiryawa baƙi ɗakunan da zasu sauka" "Calm down mana lil bro, kasan idan baƙi sukazo gurinka yanada kyau ka basu kulawa ta musamman har zuwa kwana uku, to inya Wuce hakane nauyinsu ya sauka a kanka, yanzu kayi hakuri Ni ka faɗa Min menene ke damun ka, i promise zan baka shawara me kyau. Shiru SARFRAZ yayi yana tunanin ta inda zai fara faɗawa Aayaan ya fasa auren hassu saboda wata daya gani yanzu. "Bro dama kawai inasone naga hassu saboda akwai maganganun danake so muyi da ita" "Ooh lil bro wato saboda ɗan wannan abinne ka damu kanka haka? Yanzu ka kwantar da hankalinka zansa Aunty Aseey ta turo maka ita, *Happy?* Murmushi SARFRAZ ɗin yayi tare da cewa *"Yes happy"* Hatta da ɗakin sarfraz ɗin acike yake da baƙi, don haka rasa inda zasu samu su zauna sukayi. Chan garden suka tafi suka zauna, ciro waya Aayaan yayi yayi dialling ɗin Number Aseey, ƙara biyu ana uku ta ɗauka "assalamu alaikum bro" "Wa'alaikumus salaam, Aunty Don Allah hassu zaki turomin, ina garden" Shiru Aseey tayi tana tunanin hassun yake nufi ko Nawaz. Sai daga baya tace to bari na turota yanzu. Sannan ta kashe wayar. Gama wayarsu keda wuya farouk ya kirashi, ɗaga wayar yayi tareda miƙewa yana yiwa SARFRAZ alamun yana zuwa da hannu. Da ɗan sauri saurinta ta ƙarasa garden ɗin, Sarfraz Kawai tagani bataga Aayaan ba, kuma Aseey tace mata Aayaan ne yake kiranta. Gaban Sarfraz ɗin ta ƙarasa tare da cewa yaya Sarfraz ina yaya Aayaann ɗin? Da ɗan mamaki yace mata "mezakiyi mishi? "Aunty Aseey ce tace wai yana nan yana kirana" shiru SARFRAZ yayi yana mamakin chanzawar hassun domin yanzu hundred percent ya gane itace, ga muryarta nan ma raɗau. Murmushi yayi ya miƙe tsaye tare da ƙarasawa gab da ita sannan yace "wai fushi kikeyi dani naga kin dena kulani? Nine fa SARFRAZ ɗinki wanda kike yiwa komai" "Mummy ce tace kada na kulaka, wai baka damu daniba saboda sanda mukaje Sudan har muka dawo ko sau ɗaya baka taɓa kiranmu kaji ya muke ba. Kwantar da murya yayi tare da cewa "oh mummy so takeyi ta haɗamu faɗa, amma Ni na isa nace ban damu dake ba? Ke kinsan yadda nakejinki a cikin zuciyata kuwa? Inasonki da sosai" Daɗine ya rufe hassu, tama rasa me zatayi tsabar murna "wai yau itace Sarfraz yake cewa yana sonta" Hugging ɗinta yayi tare da cewa "kwana biyu bamu ji dumin juna ba, hope banyi laifi ba?" "Murmushi hassu tayi "wane laifi zakayi bayan munsha kwana a haka sau babu adadi! Shi kuwa Sarfraz yana rungumeta yaji yanaso ya koma ruwa, abubuwan da ada ya dena ji saiyaji suna dawo mishi ɗaiɗai da ɗaiɗai, take jikinshi ya fara vibration, a hankali idonshi suka fara chanza launi sakamakon yadda kamshin jikinta da ɗumin jikinta ke ratsa shi, ga wani taushi na musamman da Fatar ta tayi. Da kyar ya ɗago yace "jeki cikin gida, anjima zan aiko miki da waya" Murna fal cikin hassu, wai yau ita Sarfraz zai siya wa waya, kuma ita yace yanaso, anya zata iya barci kuwa? Harta juya zata tafi sai kuma ta waigo "ina yaya bandi? A kasalance sarfraz yace "yana babban falour tare da yan uwan abbanku" ya ƙosa tabar gurin domin wani irin feelings ne yaji yana taso mishi gadan gadan Koda dare yayi kasa barci yayi sai juye juye yakeyi, fir barci yace besan zance ba, har saida ya samu ya tashi ya hada wa kanshi shayin lemun tsami sannan ya samu relief, ko bayan yasha beyi barcin ba sai misalin biyu da rabi na dare. Washe garima haka ya tashi sukuku, mutane sai tsokanar shi sukeyi wai ya fara zazzaɓin barin gida, nan kuwa basusan ya ƙosa akai mishi Yar mutane bane ya kwamushe ta. Cikin ƴan kwanakin nan haka yake kwana yana juyi, koyasha lemun tsamin ma a banza, beso ma koda wasa ya ganta domin daya ganta jikinshi zai harba, Shikenan babu shi babu zaman Lafiya. Ta ɓangaren Aayaann kuwa mummy ko kallon shi batayi sannan koda wasa taƙi Bari yayi tozali da Nawaz tun ranar da suka zo. Abin duniya ya ishe shi, ya rasa yanda zai yi, hakanan shima yake maneji, duk iya tunanin shi yayi na yadda zaiga Nawaz ɗin amma abu yaci tura, harta hannun Aseey yabi amma abu shiru. Rana bata ƙarya saidai uwar ƴa taji kunya, ayau ne dubban jama'a daga sassa daban-daban na kasar nan harda na waje suka shaida daurin Auren Sarfraz Muhammad da Amaryarsa Hafsat kabeer akan sadaki dubu ɗari biyu lakadan ba ajalan ba. Ango sarfraz sai zumuɗi akeyi ansha babbar riga, daga ayi nan rii da abokanai sai ayi chan rii, baki yaƙi rufuwa sai kace me tallan MacLean. Yan ajinsu na HAYATUL ISLAM saida sukayi ta mamaki da sukaga malama NAWAZ, anan ne ya shaida musu cewa itadin matar babban yayanshi ce. Gida ya cika fam sai shagali akeyi, abinci kuwa ba'a magana sai kaci ka ture duk wanda yayi maka, domin Manyan restaurant uku Aayann yaje ya bada order bayan wanda akayi a gida... Nawaz da Amarya hassu da Aunty Aseey ansha kyau an gaji, dai rangaji sukeyi daga suje chan sai suje nan. Mijin Aseey dayazo ɗaurin Aure sai ya shafe idonshi ta toka yace besan zance ba, "wallahi ki shirya don gobe ƙafarki kafata, wato ke kinzo gida sai shagalinki kikeyi nikuma ga ɗan Iska kinbarni achan sai hamma nakeyi. Iya roƙo babu irin wanda Aseey batayi mishi ba amma yace sam babu abinda zai hanasu tafiya gobe. Tanaji tana gani haka ta fara shiri, domin ya ɗauke muhsien ma ya tafi dashi hotel ɗin daya sauka, ita kanta dan idan ya tafi da ita za'a neme tane amma da Wallahi saiya rage zafi barin yadda yaga ta koma. Dayake sarfraz yace baza'a yi event ko ɗaya ba wai saboda kada a kalle mishi mata, shiyasa iya yinin biki akayi. Da yamma tayine aka fara kace nace tsakanin dady da mumy, Daddy yace akaiwa sarfraz matarsa gidanshi su tare inyaso bayan wata ɗaya sai a tura musu tsohuwar da zata rika zama dasu tunda hassu ɗin ma makaranta za'a maida ita, ita kuma mummy tace a barta a gurinta bayan Yan watannin sai su tare saboda aga kamun ludayin zaman nasu. Daga karshe dai Daddy ne yaci, nan aka jera motocin kai Amarya cikin unguwa. Nawaz kuwa anyi ruwa anyi tsaki tunda dama ita ta fito ne a matsayin yayar Amarya, shiyasa duk inda zatabi hassu na maƙale da ita. Gida dai yayi kyau iya kyau, kowa sai santi yakeyi, haka kujeru da gadon gwanin sha'awa sun dauki painting dakin dayake yadinsu milk da golden ne, ga dining ga ventilation ga ga ga hmm idan nace zan tsaya siffanta dakin saimu wuni muna abu ɗaya. Koda Yan kai Amarya zasu tafi hassu ko Irin kukan Amaren nan ma batayiba, idonta ƙemadagas. Har saida aka samu masu tsokanarta suna cewa "lallai hassu, ido yaji kwalli wato ko a jikinki, amma yarinya zaki yabawa aya zakinta ne nan bada jimawa ba. 🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *62* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* *Wannan shafin na duka masoya Sarfraz ne, much love 😍😍😍.* Su Nawaz basu daɗe da tafiya ba saiga tawagar ango sun iso suma, amma abin mamaki shine iya falour Sarfraz yace su zauna, wai babu me shiga mishi ɗakin mata ya gane musu sirri. Babu Wanda beyi mamaki ba, amma sai suka basar tare da cewa su suka kawo kansu dole yayi musu abinda yaga dama, kuma ai Aure lokacine suma sun tabbata wata rana nasu za'a yi, domin jariri ma ango ne wata rana. Saida Sarfraz ya raka su har mota sannan ya koma ɗakin Tare Da rufe ko ina da key sannan ya nufi bedroom ɗin da hassu ke ciki. A zaune ya Tarar da ita kanta da fuskarta lulluɓe da mayafi, hannuwanta sunsha lalle sai wasa da yatsun hannunta takeyi. A gefenta ya zauna tare da kama yatsun yana cewa "Hafsatul Ikraam" Shiru tayi batace komai ba, saboda hakanan taji yau tanajin nauyinshi. "My Ikraam yau kuma Sarfraz ɗin naki kikeyiwa yanga? Ko kuma kunyata kikeji? Ɗan ɗaga kai tayi alamar "eh", zaro ido sarfraz yayi 😳🤔 "wai da gaske kike ko wasa?" Namma dai shiru ta kumayi batace Komai ba. Jinjina kai Sarfraz yayi tare dayin murmushi "taɓ! Ke kunya yau zaki ƙara gaba domin nan ba huruminki bane sam, don bazan yarda ki cutar daniba" Buɗe fuskar ta yayi yana cewa "bari naga my beautiful wife's face" sauri tayi ta rufe idon tana ɗan yin murmushi mai sauti. Gaba ɗaya ya cire mayafin yana kallonta cike da shauƙi "yanzu sweet Ikraam ke duka mallakina ce? Shiru tayi bata tanka mishi ba, sakin hannuwanta yayi ya miƙe tsaye yana cewa "kinci abinci kuwa? Eh sanda zamu tawo Mummy ta bani farfesun kaji da madara amma ta zuba magani a ciki, jinjina kai kawai yayi ya shiga bayi. Brush yayi tare dayin wanka sannan ya ɗauro Alwala ya fito, Yadda ya batta haka ya dawo ya sameta bata ko motsa daga inda ya barta ba. Saurin kauda kai hassu tayi ganinshi ɗaure da towel domin gani tayi yayi mata wani iri, sarfraz yaga abinda tayi amma sai yayi kamar be ganta ba, "tashi kije kiyi wanka ki dauro alwala" To tace tare da mikewa ta nufi bayi, shikuma wardrobe ya buɗe ya ɗauko light Blue ɗin pyjamas yasa. Kayan barcin sunyi mishi kyau sosai kuma sai suka ƙara haska farar fatar shi. Falour ya fita befi minti huɗu ba ya dawo riƙe da Babbar shopping pack, ajiyewa yayi yana ciro abubuwan dake ciki. Manya manyan fresh milk ne sai gasassun kaji anyi folding ɗinsu a foil paper, sai gasasshen naman rago da kilishi. Fitowa tayi sanye da Kayan jikinta amma fuskarta da hannunta da alamun damshin ruwa, kallonta sarfraz yayi tare da cewa "meyasa bakiyi wankan ba? "Nayi" hassu tace a hankali "Kinyi shine kika maida kayan jikinki mai datti?" Chuno baki tayi alamun yanason ya matsa mata. "Okay to Shikenan jirani, wallahi saina baki mamaki cikin daren nan, Ni banida kunya shiyasa danayi wankan na fito zugudi-zugudi ɗaure da towel na wuce ta gaban ki ko?" "Wallahi idan baki koma kin kuma yin wani wankan ba kin dauro towel daina saɓa Miki sannan kuma na ɗaukeki da kaina nayi miki wani wankan. Babu shiri hassu ta burma Kofar bayin tayi ciki, ba'a fi minti biyarba ta fito ɗaure da pink ɗin towel tana ƙanƙame jikinta alamun tanajin kunya. Kwafa sarfraz yayi tare da jinjina kai Sannan ya raya a zuciyarshi "yarinya zaki gane kurenki ne" Miƙewa Sarfraz yayi ya buɗe wardrobe ya ciro Wasu Kayan barci baby pink colour, daka Kalli Kayan kasan basuda maraba da tsirara, domin shara-shara suke, rigar da kadan ta ƙarasa gwuiwa sai ɗan ƙaramin wando. Sai dogon hijab daya ciro shima. Gabanta ya ƙarasa yace "kisa wadannan sai kizo muyi sallah muci abinci mu kwanta. Tsaye hassu tayi tana ƙarewa Kayan kallo, taɓ Wato itace zata saka wadannan kayan ta tsaya a gaban Sarfraz? To wai meyasa yake yi mata haka ne? Batason tayi musu dashi tunda tasan saitasa kayan dolenta, bayi ta koma ta saka kayan sannan ta ɗora dogon hijab ɗin akai ta fito. Sarfraz na zaune sai murmushi yakeyi da alamu akwai wata ƙullalliyar daya ƙulla..... Taso tace mishi tayi Sallah amma ta kasa ganin yadda yake binta da wani shu'umin kallo, duk sai take ganin kamar ba sarfraz ɗin data saniba, har wani tsoro tsoronshi taji ya fara kamata. Raka'a biyu ya jasu sannan ya riƙa kwararo addu'oi kala daban daban sannan daga bisani ya matsa kusa da ita tare da ɗora hannun shi a saman kanta ya karanto addu'ar da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yayi mana umarni da mukaranta idan mun sai sabon abin hawa ko sabuwar amarya. Cewa yayi "bazan tambayeki komai ba domin tundaga kan alwala zan fara koya miki da kaina, Yanzu dai matso kici abinci. "Wallahi yaya SARFRAZ na koshi sosai" "Okay to amma Kisha madarar mana ko kaɗan ce, Nima ita zansha don Nima a ƙoshe nake" Be jira me zataceba ya buɗe robar ya saka cokali a ciki tare da miƙa mata, shima ɗaya ya buɗe ya fara sha. Saida yasha da yawa sannan ya ajiye a gefe daidai itama hassu tana ajiye Tata. Tashi muje mu kwanta! Miƙewa tayi tana son tahau saman gadon da hijab ɗin jikinta, ai kuwa da sauri sarfraz ya chafke hijab ɗin ta baya tare dayo baya da ita, kamar ta zunduma ihu sanda taji ya suɓale mata hijab ɗin daga wuyanta. Saurin shigewa jikinshii tayi saboda kada ya kalleta a yanda take, shikam sarfraz bema bi takanta ba ya rungumeta zuwa kan gadon, Saida ya kwanta Sannan ya matseta a ƙirjinshi sosai yaja duvet ya rufesu dashi. Ahankali jikinsu ya fara musanyar dumi, ba'a ɗauki lokaciba komai nasu ya haɗe guri ɗaya, tundaga kan turare, numfashi har zuwa hucin jikin juna. Tuni hassu tayi barci saboda yadda ɗumin jikin sarfraz ke ratsa duka jikinta dama gashi garin akwai sanyi sosai. Shikam sarfraz sam ya kasa barci, tun yana ƙokarin yakice feelings ɗin daya fara taso mishi har saida yasha kanshi, gadan-gadan yakejin kamar ciwon cikinshi zai dawo mishi, wata zuciyar ce tace "ga magani a kusa dakai me kake jira? Halal ɗinka ce fa, kuma tana sonka sosai. Sai yaji tausayin Hassu ɗin yana neman kamashi, amma sai wata zuciyar tace hassun da ka sani! Ka manta yadda ta koma ne yanzu? Ji yayi zuciyarshi tayi na'am da shawarar, Ahankali ya zame rigar dake jikinta tare da subale short ɗin jikinta, shima beyi sanya ba ya cire duka kayan dake jikinshi, haɗe ta yayi da jikinshi yana sauke ajiyar zuciya, sosai jikinsu ya haɗu har wani Kamar shock Sarfraz yakeji yana bi mishi jiki saboda yadda fatarsu ke gogar ta juna. Tun yana iya daurewa har yakai maƙura, kirjinta ya fara dora tafukanshi akai yana yawo dasu, da a hankali yakeyi amma Yadda jikinshi ke amsar sakon saiya birkice bema tuna cewa ita yarinya ce ba. Kamar daga sama hassu taji ana yamutsata ga wani zafi da kirjinta keyi mata, firgigit ta buɗe idonta, amma abin haushi babu abinda ta gani Sakamakon Sarfraz ya kashe duka hasken ɗakin. Ƙaruwa abinda takeji yayi, sosai ta razana saboda yadda take jiyo gurnanin Sarfraz.. cikin Muryar tsoro tace "yaya Sarfraz don Allah kadee..na a tso..ro.. na..ke..ji Taɓ Sarfraz befa san a inda yakeba, be sanma me takeyiba balle yaji me take cewa. Ganin yadda yayi banza da ita kuma sai dada birkitata yakeyi tundaga kan gashin kanta har zuwa kowane sassa na jikinta sai ta fashe da ihu tana cewa "wallahi ka bari banaso, wayyooo mama! Nidai ka bari banaso. Kukan da takeyi sai ƙwaƙwalwar Sarfraz ta maidamai shi kamar tana yimai ne don ya ƙara kaimi. Ai kam da duka hannuwanshi ya tallabo kanta ya haɗa bakinsu guri ɗaya, take ihun da hassu takeyi yayi ɗif illa Shure shuren data cigaba dayi, tuni idonta ya cika da ƙwalla tana zubowa babu ƙaƙƙautawa don ita bata taɓa ganin bala'i a fili irin wannan ba. Yadda yake kissing ɗinta gaba ɗaya lebenta zafi sukeyi mata, ji take kamar zai cinyesu tsabar yadda yake tsotsonsu kamar ya samu minti. Bata ƙara firgita ba saida taji yana ƙoƙarin tura mata yatsa a ƙasanta, iya ƙoƙari tayi amma ta kasa hanashi saboda yadda ya sakin mata nauyi Gashi bakinsu na haɗe Guri guda. Azaba taji har ƙwaƙwalwarta sannan ga zugin da gurin yakeyi mata kamar an barbaɗa mata barkono, shikam Sarfraz be tsaya ba Saida yaji duka yatsan ya shige ciki, sosai ya fara wasa da yatsan yana fitar dashi yana maidawa, kuma bawai a hankali ba iya karfinshi domin Yanzu abinda yakeji shi kawai ya fuskanta gaba-daya. Azabar da Hassu takeji bata taɓa jin irin taba tunda ta tsinci kanta a duniya, mintsinin shi ta fara yi a baya tare da tastaska mishi duka. Shikam Oga Sarfraz ko a jikinshi, sakin bakinta yayi ya ɗora nashi bakin a saman kirjinta yana tsotsa saikace beby yaji yunwa. Wata sabuwar azabar ce ta kuma zirartarta domin komi da zafi zafi yakeyi. Kuka takeyi amma sam ya kasa fitar da sauti saboda yadda ta wahala ga bakinta da harshen ta kamar ya tsage biyu tsabar zugin datakeji yana yi mata. Ta jigata iya jigata hakan yasa tayi shiru kawai tana sauraron azabar da Sarfraz yake gana mata, yatsanshi taji ya mayar ƙasanta yana jagwalgwalawa, aikuwa har tsakiyar ƙwaƙwalwarta haka taji wani uban zugi yana ziyartarta. Bata tabbatar Allah ɗaya bane saida taji wani uban kakkauran ƙaton abu mai ɗumi yana neman ratsa mata jiki, aikuwa babu shiri taji muryarta ta washe wani karfi yazo mata, ihu ta zabga "wayyooo sarfraz don girman Allah kada ka kasheni, wallahi na fasa auren!!! Wallahi bana sonka. Ɗago da kirjinta tayi don neman agaji amma sai Sarfraz yasa hannu ya dannata ta koma baya, be jira wani abu ba ya tura kanshi da iya karfinshi. Wani irin ihu hassu ta saka take kuma jikinta duka ya saki alamun ta sume. Shikam jinshi da yayi a inda be taɓa tunanin akwaishi a duniya ba yasa ya bada kaimi wajen entrusting, Saida ya tabbatar length Dinshi ya shige duka sannan ya fara in and out... (Jama'a Sarfraz zai kashe ƴar mutane, nifa na gaji da ganin wannan irin azabtarwar) Sosai Sarfraz ya dage da abinda yakeyi Kamar Allah ne ya aikoshi har kuka yakeyi ba tare daya saniba, bema lura da halin da hassu ɗin take cikiba illa dai ya maida hankalinshi ga sakon da ƙwaƙwalwarshi ke watsawa duka jikinshi. Wani uban ƙara ya saki tare da cewa "Ikraam zaki kasheni fa", da sauri da sauri yake sauke numfashi kamar wanda yayi gasar tseren duniya, sai kuma jikinshi ya saki lokaci ɗaya. Yafi minti goma a haka sannan daƙyar ya tashi daga kanta yana ɗago ta, jin jikinta yayi gaba ɗaya ya saki babu alamar numfashi a tare da ita, aikuwa babu shiri ya dire daga gadon yana kunna hasken ɗakin. Zaro Ido waje yayi ganin gaba ɗaya farin zanin gadon yayi kaca kaca da jini, itama hassun kwance kamar matacciya. Ƙaramin fridge ɗin dake gefe ya buɗe ya ɗauki ruwa roba ɗaya. Cikin hanzari yake buɗe robar ruwan tare da nufar gadon, dagota yayi ya shafa mata a fuska amma ko motsi batayi ba, ruɗewa sarfraz yayi sosai ganin yadda jikinta yake a sake. Tattarota yayi duka a jikinshi ya rungumeta yana ƙara zuba mata ruwan a fuska, saida yakai kusan minti goma a haka Sannan yaji tayi wata wawiyar ajiyar zuciya da shesheƙar kuka a tare. Wani Irin daɗi ne ya ziyarci zuciyar Sarfraz domin ba ƙaramar damuwa ya shiga ba. Ta tashi amma ta kasa furta koda kalma guda ɗaya, jinta takeyi kamar ba ita ba, a Yadda takeji dama zata mutu ta huta, babu gaɓar da bata yi mata ciwo a jikinta uwa uba kuma ƙasanta da takeji kamar an tura mata tabarya me atarugu an barta a jiki. Kirjinta ma kamar zai zazzage ya fado ƙasa, tama kasa buɗe idonta saboda yadda ya kumbura. "Ikraaam i am sorry! Pls ki yafe mini wallahi ba'a hankalina nayi miki wannan aika aikar ba, na tuba. "Wallahi ina matuƙar ƙaunarki a yanzu na Daɗa tabbatar wa cewa kece rayuwata bazan taɓa iya rayuwa ba idan bakya kusa Dani. Sosai yaketa faɗa mata daɗaɗan kalamai tare da shi mata albarka, inda ita kuma hassu takejinsu kamar saukar aradu a kirjinta, domin ta riga data rantse a zuciyarta babu ita babu SARFRAZ, domin ko da datake cewa tana sonshi batasan cewar shi mugu bane sai yau. Haka suka kwana yadda suke, saida aka kira sallar asuba ne sarfraz ya ajiyeta a hankali sannan ya shiga bayi yayi wanka ya ɗauro Alwala ya fito. Rasa yadda zai yi da Ita yayi sai kawai yace bari ya fara yin sallar saiya san yadda zaiyi da ita. Koda ya idar da Sallah saiya shiga bayi ya cika bathrub 🛁 da ruwan zafi Sannan ya dawo ya ciccibeta yashiga da ita ya saka ta aciki. Aikuwa babu shiri ta zabga wata Uwar ƙara saboda wata uwar azaba dataji tana ratsata tako ina. Jikin SARFRAZ har rawa yakeyi yasa hannu ya cire ta daga Ruwan, duk dabarar dazaiyi yayi amma taki yarda saima Allah ya isa data fara jera mishi tana cewa ya maida ita gida wallahi babu ita Babu shi har abada. Jin kalaman da takeyi ba ƙaramin tashin hankali yashiga ba, ya rasa yadda zai yi, waya kawai ya dauka amma saiya rasa wa zai kira, Number Aayaan yayi dialling, yana ɗagawa saiya Fara kame kame "yaya dama na kira wayar Aunty Nawaz ne shine bata shigaba, don Allah hassuce takeso ta ganta. Sosai Aayaann ya gane aika aikar da sarfraz yayi, sai kawai yayi murmushi yace, "to bari nakai mata wayar" "Ehm yaya inda hali don Allah tazo gida ne" "Okay to Bari na kawota" Muryar Sarfraz har harɗewa takeyi wajen cewa "Nagode yaya Allah ya saka da alkhairi" °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Nawaz na kwance tana sheƙa barcinta na gajiya karar wayarta ya tada ita. Koda ta duba sai taga Ashe Aayaan ne, ɗagawa tayi ta kara a kunnenta sannan cikin Muryar Barci tace "yaya Barka da safiya fatan mun tashi Lafiya" "Lafiya Lau sweet heart, don Allah so nakeyi kizo yanzu amma kada ki bari kowa ya sani, zamuje gidansu SARFRAZ ne bashida lafiya yanzu ya kirani. Ai babu shiri Nawaz ta tashi zaune tana cewa gatanan zuwa yanzu, hijab kawai ta zura a saman doguwar rigar barcinta ta fita zuwa falour. Cikin Sa'a suka haɗu da Aayaan ɗin a falour, Binta yayi da kallo yana kunshe dariya tare da yin tunanin abinda zatayi idan taje taga abinda sarfraz yayi wa hassu domin ya santa da kunya. Gaba ɗaya ko a cikin motar hankalin Nawaz a tashe yake domin mamaki takeyi meya samu Sarfraz ɗin daga jiya zuwa yau. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *63* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Aayaann nayin parking bata jira komai ba ta fita waje tayi cikin gidan. Daidai zata buɗe ƙofar faloun shima SARFRAZ ya buɗe har saida suka bangaji juna, cikin sauri tace "Sarfraz wai bakada lafiya?" Rimi rimi Sarfraz yayi da ido yace "No Aunty bani bane banida lafiya Ikraam ce" Tana tsaye ya fice zuwa harabar gidan inda ita kuma tasa kai cikin faloun, "hassu! hassu!! Hassu!!! Nawaz keta ƙwalawa hassu kira amma shiru. Cikin bedroom ɗin ta nufa domin tafi zaton tana nan, sam bata kawo komai ba a ranta na cewa ko wani abune ya faru tsakaninta da sarfraz ba. Koda ta tura ƙofar dunɗum haka taga ɗakin sai dai akwai ɗan alamun haske "hassu kina ciki?" Nawaz ta faɗa tana karasawa kusa da window don buɗewa, shiru dai ba'a bata amsaba. Zuge labulayen tayi zuwa gefe, take haske ya Bayyana a kowane lungu da saƙo na dakin, waigowa Nawaz tayi don ganin ko hassun barci takeyi har yanzu. Aikuwa saida idonta ya kusa faɗowa ƙasa saboda Yadda ta zarosu waje, kirjintane yahau dukan uku uku tana jinta kamar ta ruga a guje sakamakon abinda idonta ya gane mata, babu irin abinda zuciyarta bata raya mataba.. Cikin sanɗa ta ƙarasa bakin gadon tare da taɓa bargon da hassu take ɗuƙunƙune aciki, wani hucin zafi taji hannunta yayi alamun hassu ɗin tana fama da matsanancin zazzaɓi. Ƙarfin hali tayi ta janye bargon, aikuwa babu shiri ta maidashi sakamakon ganin hassun babu koda ɗan kampai, kar kar kar jikinta ya fara rawa ga kirjinta dayake dukan uku uku, tama rasa me zatayi tsabar tsoron yanda taga hassu ɗin, babu abinda yafi tada mata hankalima kamar uban stain ɗin jinin data gani duka gadon. Lahaula wala quwwata illah billah ta fara maimaitawa a zuciyarta tana yiwa Allah tasbihi, a hankali a hankali ta fara jin nutsuwa tana saukar mata a zuciya Sannan fargabar taɗan ragun mata. Wardrobe ta buɗe ta dauko fallan zani sannan ta ƙarasa bakin gadon tare da zame bargon, zanin ta ɗora mata a jikinta sannan a hankali ta ɗago kanta "sannu hassu, Don Allah kiyi hakuri kinji" Hawayene taga yana zarya a idon hassu ɗin, daga wannan sai wannan, sosai hassu ɗin ta bata tausayi Domin tasan itama tsoro takeji balle wannan Yar mitsitsiyar yarinyar. Pillow ta janyo tare da ɗora kan hassu akai sannan ta tattara bargon ta saukeshi gefe, zanin gadon ta yaye gefen da babu hassu ɗin Sannan kuma ta maida hassu ɗaya gefen, daukeshi tayi duka ta haɗa da bargon ta shiga bayi ta zuba a washing machine ta zuba liquid soap sannan ta kunna. Ɗakin ta dawo ta samu hassu sai sharɓar hawaye takeyi, gefenta ta zauna tare da janyota jikinta "hassu nasan kin cutu amma don Allah kiyi hakuri, kuma dama auren kenan ai, sai hakuri yau da gobe zaki saba balle Allah ya hadaki da miji mabuƙaci. Cikin dashashshiyar murya hassu tace "Aunty Nawaz wallahi SARFRAZ bashida imani ko kaɗan, bakiga irin azabtarwar dayayi mini ba, babu irin ihun neman agajin da banyi ba amma ko'a jikinshi" "Yi shiru! Dena faɗa, kiyi hakuri, kuma zanyi mishi magana sosai, hakan dayayi sam be daceba, amma yaci darajar cewa shi mijin kine kinji?" Hassu na sharɓar kuka tace "tab wallahi badaniba, ai wallahi sai dai ya nemi wadda zai cigaba da ganawa azabar amma wallahi Ni gidanmu zani Don NAGAMA AUREN" Daurewa Nawaz kawai takeyi amma ita kanta kamar ta ruga da gudu takeji, "yanzu zaki iya tashi? Inaso kiyi wanka ki samu ki gasa jikinki saikici abinci kisha magani. "Aunty Wallahi ko motsa jikina nayi kamar zan mutu nakeji saboda azaba" "To bari nazo" cewar Nawaz tare ta miƙewa ta shiga bayi, ruwan zafi ta haɗa ɗan dai-dai yanda tasan bazai cutar da hassu ɗinba Sannan ta koma gurin hassun ciccibarta tayi suka shiga bayin sannan a hankali ta sakata a cikin ruwan zafin tare da cewa "pls nasan Akwai zafi Amma don Allah ki daure" Cije baki hassu take tayi ga wani uban gumi da yaketa karyo mata, duk jikinta yayi ja alamun tasha matsa ga fuskarta da hancinta duk sunyi pink barinma laɓɓanta da sukayi jajir kamar jini zai zubo. Sannu kawai Nawaz ke jera mata fuskarta ɗauke da alhini. Ayanda hassun ke cije baki Nawaz tasan hakuri kawai takeyi don babu yanda zatayi ne. Duk jikinta yayi jajir alamun tasha damƙa, haka fuskarta da hancinta duk sunyi Pink tsabar wahala, bakinta kuwa yayi jajir kamar jini zai fito. Saida ta daɗe sosai a Ruwan Sannan Nawaz tace "bari a chanza miki wani Koh? Marairaice fuska hassu tayi "Aunty Don Allah kiyi hakuri ki bari Sai anjima sai a kuma yi" Murmushi Nawaz tayi Domin tasan hassu ɗin ma tayi ƙokari, "to Bari na chanza miki wanda zakiyi wankan tsarki yanzu" Tana tsaye harta gama wankan, babu laifi ta iya sosai sai dai abinda ba'a rasa ba, wani ruwan ta chanza mata tace tayi wankan sabulu ta Daura alwala Idan ta gama saita kirata ta ɗauke ta. Dakin ta koma ta chanza zanin gado sannan ta gyara guraren da ba'a rasa ba sannan ta shiga kitchen. Ruwan lipton ta ɗora haɗe da Kayan kamshi kala kala Saboda tasan bakin hassu ɗin babu daɗi, harzata fita daga kitchen ɗin ta hango ledar kajin da SARFRAZ ya siyo jiya, tsayawa tayi ta gyarasu ta zuba a oven ta saita time sannan ta koma ɗakin Don ganin ko hassu ta gama wankan. Tana shiga taji hassu na cewa "Aunty na gama" ai da sauri ta ƙarasa bayin tare da chukuikuyeta a cikin towel ta daukota ta direta akan gado. Sosai ta taimaka mata ta gyara jikinta, riga da skirt ɗin wani jan material tasa, ɗinkin das ya zauna ajikinta kamar anan aka dinkasu Sannan tadanyi mata light make-up daga powder sai dan lip stick kaɗan da kwalli, ruwan zafin ta Kawo mata tace tasha saboda cikinta ya warware kuma bakinta yaɗan yi mata daɗi, nan ma saida akayita gwagwagwa sannan tasha kaɗan. Naman kazar nema tadanci da yawa sannan tace ya isheta, gyara zama hassu tayi Domin ta gaji da zaman ma gaba ɗaya "Aunty jikina duka ciwo yake yimin Wallahi barinma gurin fits...... Toshe mata baki Nawaz tayi Kafin ta ƙarasa faɗar Abinda tayi niyyar faɗa. "Sannu kinji Zai dena gaba ɗaya, Yanzu Bari na kirasu a waya in faɗa Musu su tawo miki da magunguna. Tsalle hassu tayi ta dire akan itafa bazata jira su dawo ba, domin ita gidansu zata tafi. Mamaki ya hana Nawaz motsi domin itafa hassu bilhaƙƙi take nufin gida zata, "hassu wai idan kinje gidan me zakiyi? Ko kuma ma ince me zakice musu yasa kin dawo" Nawaz ta faɗa tana tsare hassun da ido domin taga iya gudun ruwanta. "Faɗa musu abinda ya faru zanyi kawai, Kinga sai a ɗauki mataki, idan zai dena sai in dawo muci gaba da zama, idan kuma bazai dena ba sai kowa ya kama gabansa. "Yanzu hassu duk soyayyar da kikewa Sarfraz ɗin dama ta ƙarya ce? Kuma naga har dai don wannan ne basai anje gidaba za'a iya yin sulhu, kuma nasan zai dena tunda yana sonki, kuma ko wannan ma nasan akasi aka samu" "Wallahi Aunty ba akasi bane yana sane Domin babu Irin duka da cizon da banyi mishi ba amma yayi banza dani, nasan idan aka barni dashi wata rana kasheni zaiyi. Sosai Nawaz ke ganin tsantsar wauta da yarintar hassu a fili, ita tama rasa me zatace mata Yanzu. Miƙewa tayi zataje kitchen sai kuma ta waigo "hassu ina jakar da kika riƙe ranar biki?" "Tana cikin drawer menene? "Dama akwai ragowar Diclofenac ɗin da Aunty Aseey tasha saboda aciki ta saka, Kinga kema zaiyi miki amfani yanzu, wace drawer ce in ɗakko? Nuna mata hassu tayi da hannu, ita kuma Nawaz ta ciro maganin tare da buɗe fridge tana ɗauko ruwa mara sanyi, Guda biyu ta ciran mata tare da buɗe ruwan tana miƙa mata... Nawaz takai awa kusan uku da zuwa amma har yanzu shiru su SARFRAZ basu dawoba, su Hassu Diclofenac ya Fara aiki domin harta saki tana ɗan wasanta sai dai tafiyar ce har yanzu Saida dabara. Jollof rice Nawaz ta dafa musu domin ta gaji da zama babu abinda takeyi, sun gama ci kenan saiga su SARFRAZ sun dawo. Ba hassu Wadda abin ya faru da ita ba hatta Nawaz saida taji zuciyarta ta bada dararam dam dam, don ita Yanzu tamafi hassu ɗin jin tsoro. Saida ta daburce da Aayaan ya ƙaraso kusa da ita, kallonshi takeyi tana kallon SARFRAZ, babu ta inda be fishi girma da murdewar jiki ba, wani irin tsinkakken miyau ne taji yana ƙokarin Wuce mata ta ƙaramin makoshi, ai kam babu shiri ta haɗiye shi. Itakam duk randa Aayaan ya damƙeta ya zatayi kenan? Ji tayi tsoron da takeji na Aayann data samu ya gushe mata na ƴan kwanaki ya dawo mata sabo fill, take zuciyarta ta fara bugawa da sauri da sauri. "Sweetheart yanaga Kamar bakida lafiya? Meya faru?" Aayaann yace idonshi nakan Nawaz yana nazarin ta. "Babu komai kawai dai ji nayi bana jin daɗi" Nawaz tace muryarta na ɗan rawa "Malam ka matsa kusa dani Wallahi, tunda kai mugune kuma azzalumi mara tausayi" A tare Nawaz da Aayaan suka waiga inda suka jiyo muryar hassu na shatatawa Sarfraz rashin kunya. Marairaice murya Sarfraz yayi "haba Ikraam bana baki hakuri ba! Kuma kinga nace bazan kuma ba ai. "Nawaz kuwa ji tayi Kamar ta zunduma da gudu tabar ɗakin saboda Yadda hassu da SARFRAZ suke taɓara, tasan ko makawo ya shafa dole zai gane abinda ya faru. Ɗage gira Aayaan yayi "yadai Madam C.A Maigoro? Naga kina zufa? Shiru dai Nawaz tayi tabishi da Ido tana kallon shi don batasan me zatace ba. "Wallahi Ni kada ka daukeni, kabarni zan iya" "No Ikraam bazaki iya ba, kin manta akwai ciwo a jikinki sosai, kumafa kalli yadda kike tafiya daƙyar " Maganar Nawaz Kwarewa tayi, take tari ya turnuke ta, aikuwa da gudu tayi kitchen tana haki, shikuma Aayaan Mai zaiyi inba dariya ba, Duk ya gama lura da yanayinta gaba ɗaya, kuma ya gane tsoro ne tsantsa ke cinta da fargaba, kamar ya miƙe ya bita sai kuma ya fasa domin ya gane tarinma ƙakaloshi tayi Kawai donta gudu daga falourn. Magungunan da suka siyo Sarfraz ya ciccirarwa hassu tare da bata tasha, sai wani nan nan yakeyi da ita, "anjima Doctor tace zatazo ta Duba jikinki, saboda Kada taje ko kinji ciwo da yawa. Shidai Aayaan har mamakin Sarfraz yakeyi, ya lura sam bayajin Kunyar shi ko kaɗan, Kodayake gani yakeyi shima ya rigada yasan komai And kuma dama Aayaan ɗinne ya Fara nuna mishi cewar sun zama ɗaya. Kamar me sanɗa haka Nawaz ta fito daga kitchen ɗin riƙe da babbar warmer da plate guda biyu da cokali. A tsakiyar center table ta ajiye Sannan ta zuba, kitchen ta koma ta fito riƙe da ruwa da kwalin five alive a saman tray da tumbler guda biyu. "Ga abinci Bismillah nasan har yanzu da kyar in kun karya" "Wallahi Aunty kamar kinsan wata uwar yunwa ce ke damuna yadda kikasan ban taba cin abinci ba" cewar sarfraz yana miƙewa kusa da hassu Don karasowa kusa da abincin. Guri Nawaz ta samu ta zauna kamar gunki, ko ƙwaƙwaran motsi ta kasa yi, duk fargaba ke cinta a Cikin zuciyarta. "Aunty zoki mikar dani muje bayi ki kuma gasa min jikin, don naji kamar ya fara min tsami" "Wai meke damun hassu da SARFRAZ ne? Wallahi da nasan abinda zanzo suyi ta mini kenan da ban zoba, Sai neman kiramin ruwa sukeyi. Miƙewa tayi ba tare data ce Komai ba ta kama hannun Hassu ta miƙar da ita tare da ciccibarta suna shiga cikin bedroom ɗin. Sai bayan kamar minti talatin suka fito hassu ta chanza kaya, "inaso na tafi gida" nawaz tace batare data kalli inda Aayaan ɗin yakeba, domin wata irin kunyarshi takeji sosai. "Okay to bari nazo na kaiki" Aayaan yace yana ƙoƙarin sai sun haɗa ido. Knocking sukaji anayi a kofar falourn, koda Nawaz ta duba sai taga ashe doctor ce harta ƙaraso. Bata guri tayi ta shigo tana gaisheta, "wacece majinyaciyar? Hassu Nawaz ta nuna da hannu. "Ayyah Sannu ƴata! Ya jikin naki? "Da sauki" hassu tace. " Ku muje ciki inaso na dubata dakyau" Bedroom ɗin suka shiga inda Doctor ɗin tasa hassu ta cire short ɗinta ta duba jikinta, "dole Sai anyi ɗinki gaskiya saboda kinji ciwo kuma yayi zurfi da yawa ba Lallai ya haɗe da kanshi ba.. Jikin Nawaz ne ya ɗauki rawa, take ta ƙara tausayawa kanta tana jin kamar itama tace ta fasa Auren. Duk tananan tsare doctor tayiwa hassu allurar Barci har zuwa inda ta gama mata ɗinkin, "Yanzu ƙoƙarin da za'a yi shine ta riƙa shiga Ruwan dumi, kuma a ɗan riƙa zuba gishiri kaɗan a ciki, and bayan kwana shida zan dawo in kwance ɗinkin, kuma Don Allah kada a tasheta Daga barci nan, abari saita tashi da kanta Domin anason jikinta yayi relaxing sosai domin da gani tasha wuya. Jinjina kai kawai Nawaz ke iyayi. Har gate Nawaz ta rakata dayake tun a Asibitin Aayaan ya gama biyan charges ɗin harda na Doctor ɗin. "Sarfraz tace wai Don Allah kada a tasheta a bari ta tashi da kanta saboda wai tana buƙatar hutu. "To Aunty In'sha Allah bazan tashetaba" "Yaya Aayaann zo ka kaini gida pls banaso Aunty Aseey ta tafi batare da munyi sallama ba. Miƙewa Aayaan yayi tare da cewa SARFRAZ "sai munyi waya Bro, Allah ya bata lafia" Har bakin mota sarfraz ya rakosu yana ta yiwa Nawaz godiya, Domin yasan ba ƙaramin taimaka mishi tayiba, Don shi rasa me zai wa hassu ɗin yayi. Koda suka ɗauki hanya sai Aayaan ya rage speed ɗin motar tare da kallon Nawaz yana murmushi "sweetheart ni yaushe za'a bani Irin wannan damar da Hassu taba Sarfraz? Ko bakyason mu cikawa mummy burinta na samun yara da yawa daga gurin mu? "Kunya gaba ɗaya ta dabaibaye Nawaz tama rasa me zatace. Sosai Aayaann ya lura da halin data shiga amma be nuna mata ba, to ko mu wuce hotel ko guest inn kawai Yanzu? Kinga sai kuyi jinyarku tare da hassu ko? Ina yiwa kowa fatan ALKHAIRI, naga wannan kaunar, shin batayi min yawa ba kuwa??? Naga texts, na amsa kira naga online message ɗin da bansan adadinsu ba, Nagode Nagode sosai sosai Allah ya bar ƙauna da zumunci. Kwana biyune abubuwa suka cikurkuɗemin wallahi, amma In'sha Allah komai yazo ƙarshe. *MATAR RASHEED* ✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *64* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Shiru Nawaz tayi tana kallon shi da gefen ido, addu'a takeyi azuciyar ta "Allah dai yasa bada gaske yakeba, Duk saitaji zaman motar ma ya isheta. "Madam bakice komai ba?" Namma dai tsit tayi batare da tace komai ɗin ba illa wasa da taketayi da yatsun hannunta. Ganin halin data shiga yasa Aayaan ɗin yin shiru ya kyaleta, amma a zuciyarshi yana cewa "sarfraz ya kuma maida min da hannun agogo baya, da harta fara sakin jiki dani sosai amma yanzu tsoro ya dawo sabo fill" Ita kuma Nawaz babu abinda keyi mata yawo a zuciya illah yadda taje ta tarar da hassu da farko hajaran majaran kamar gawa "yanzu ace ƙaramin yaro kamar SARFRAZ ne yayi wannan aika aikar to babba kamar Aayaan ya zaiyi kenan?" Cewa tayi "wayyo nashiga uku na wallahi" Ashe a fili tace bata saniba, jan birki Aayaan yayi tare da cewa "sweetheart shiga uku kuma? Meya faru? rimi-rimi da ido tayi don tama rasa wace ƙarya zata rantaɓa mishi Sai kawai tace "Ni ummina nakeso nagani" "Is that the only problem? Aayaan yace yana son gane gaskiyar abinda take nufi Gyada kai Nawaz tayi alamun "eh" "Okay to kibari muje gida yanzu zaki ganta, ai sai gobe zasu tafi Koh? "Eh da yau zasu tafi amma mummy tace su bari gobe akaisu " "Okay hmmm ai Mummy akwai son baƙi, don ma tasan idan tace ta zauna ba zama zatayiba to Wallahi da cewa zatayi su zauna tare" Murmushi Nawaz ɗin tayi sannan tace "ai hakan yanada kyau sosai, kuma Ni Wallahi duka dabi'un Mummy suna burgeni, akwaita da son jama'a da mutuntasu Daɗi sosai Aayaann yaji a ranshi ganin Nawaz ta ɗan saki har suna hira. Cigaba da tuƙin shi yayi yana sako mata zance jefi jefi. Koda suka isa gida be bari ta fita daga motar Ba saida ya ɗan jata da hira yanata tsokanarta "wai yaushe ne matar nan tawa zata yarda da cewa ita ɗin mata tace? "Nayarda mana" Nawaz tace tana murmushi "Anya kuwa sweetheart maganar nan har zuci take kuwa?" Murmushi ta kumayi batace Komai ba. Sai Sannan ya buɗe mata motar suka fita a tare, a bakin kofar falour suka ci karo da kakar Nawaz "A'a megida daga ina kuke ne, tun ɗazu sai cigiyarku akeyi amma babu ku babu alamun ku, nifa nafara ganin alamun rashin adalci a wannan tafiyar, ka ɗauke Amarya kun fice kabar uwargida ko kuɗin karin kumallo baka bar mata ba. Murmushi Aayaan yayi tare da saka hannu a aljihu yana ciro kuɗaɗe, a cikin hannun ta ya zuba kuɗin Sannan ya haɗe hannunshi guri ɗaya yana cewa "uwargida Sarautar mata don Allah ayimin afuwa, na tuba nabi Allah na biki" Kyalkyalewa da dariya Ammah tayi tana cewa "Ato Shikenan an yafe maka ka fanshi kanka, aini nazata har za'a juyamin baya ne. "Wane Ni? Ai ban isa ba, kin manta kece nishaɗi na! Ita dai Nawaz raɓewa tayi ta barsu nan ta shige ciki don taga abin nasu bame ƙarewa bane. Tana shiga ta tarar da Aseey ta janyo trolly fuskar nan a kumbure kamar an watsawa flour yeast. "Aunty kardai kice min har kin shirya? "Hmm sis wallahi baban muhsien yaso ya ƙure nine, nayi nayi dashi ko kwana ɗaya ya ƙaramin don naje gida na kwaso ragowar kayana amma ya baɗe idonshi da toka yace shi sam besan zancen ba, wai kafata ƙafarshi. "To Aunty ai yayi ƙokari wallahi, kin fa daɗe da zuwa, Allah da wanine bazai yarda ba. "Hmm amma wanin ba irin mijinkiba Koh? Don naga alamun kece ma mijin don sam bayason ɓacin ranki, yayarda shi ya cutu da ranki ya ɓaci. "Kai Aunty! Allah ba haka bane, kawai dai shi yanada tausayine sosai" "Hmmm mu namu mazajen basada tausayin kenan Koh? Zaro ido Nawaz tayi "Allah Aunty ba haka nake nufi ba Wallahi.. Bata ƙarasa faɗan Abinda zata faɗa ba saiga Mummy ta shigo riƙe da ƙaramar jakar hannu tana miƙawa Aseey, kallon Nawaz tayi "daughter Kawai sai mu nemeki mu rasa da sassafe, ina kukaje ne? "Ina kwance da safe yaya Aayaann ya kirani a waya wai inzo muje Gidan Sarfraz wai bashida lafiya, saida mukaje naga ashe hassu cema. Saida ta faɗi hakan kuma kunya ta rufeta ta fara sunne kai. Basarwa Mummy tayi "ayyah ai gajiyar biki ce nasani, amma ai jikin da sauƙi yanzu ko? "Eh taji sauƙi sosai don ko yanzu da muka tawo tana barci. Juyawa Mummy tayi ta fita da sauri don tanaso ne taje ta faɗawa Mummyn SARFRAZ cewa SARFRAZ yayi aika aika ya kamata aje a duba yarinyar mutane, kuma kada abari kowa yaje balle azo ana yada ƙananun maganganu. Bayan mummyn Aayaan ta gama faɗawa Mummy jikinta har rawa yake yi wajen dialling ɗin number Sarfraz. Cikin Sa'a kuwa kiran na shiga ya ɗaga "hello mummy" "SARFRAZ ina hassu ɗin take? Ina fatan dai tana lafiya? "Eh da sauki, barci ma takeyi" "Kenan batada lafiya Koh? "Eh mum! amma Aunty Nawaz da yaya Aayaan sunzo, ta kula da ita sosai, shikuma mukaje asibiti muka tawo da Doctor ta duba ta" "Amma dai jikin da sauƙi sosai Koh?" "Eh mum amma dai wai har ɗinki Doctor ɗin tayi mata" "Subhanallah!!! nashiga uku! Sarfraz dama bakada hankali? Kayi irin wannan aika aikar sannan ka iya faɗa Min Babu ko jin kunya balle nauyi.. "Mum kefa kika tambayeni, kuma Bansan me zance Miki ba, kumani banaso nayi miki karya" "Okay to Yanzu tana tashi daga barcin ka kawo min ita" "To mum In'sha Allah zan kawo ta" Sannan ya kashe wayar Juɓur mum ta Zauna a kujera tare da haɗa tagumi hannu biyu "gaskiya Sarfraz akwai sauranshi, shiyasa fa na dage akan Abar min yarinyar nan a gidan nan amma dadynshi ya ɗaure mishi gindi wai abashi matarshi su tafi. Murmushi Mummyn Aayaan tayi tare da cewa "to ai Yanzu aikin gama ya gama, sai dai akawota a kula da ita kada ya tasata agaba, don nasan idan aka barsu guri ɗaya ba lallai abar ɗinkin ma ya warke ba. Girgiza kai Mummyn SARFRAZ tayi "hmmm ni kadai nasan halin danake ciki wallahi, amma gaba ɗaya tunda naji maganar nan zuciyata ta tsinke, yanzu babu Ni babu samun sukuni sai naga yarinyarnan a gaban idona. "Yaran namune na yanzu sai hakuri wallahi" cewar Mummyn Aayaan. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Zaune Nawaz suke a mota ita da Aayaan bayan sun kai Aunty Aseey gidan yayar baban muhsien, don acan yace taje ta sameshi daganan saisu wuce Abuja, washegari kuma saisu ɗaga zuwa England. "Sweetheart inaso nima naje England fa nanda Three days, kuma Gaskiya zan daɗe acan, Don a ƙallah zan iya kaiwa Three months" Duk sai Nawaz ɗin taji babu daɗi saboda tasan Yanzu idan Aayaan ya tafi haka zatayi ta zama kamar mayyah, tunda Aunty Aseey ta tafi gashi Maiduguri zasu koma balle ta riƙa zuwa koda gidansu SARFRAZ ne. "Yadai Madam! What happened?" Aayaann yace yana kallonta sosai A sanyaye Nawaz ɗin tace "Babu komai, kawai dai Naji Babu daɗi ne da kace zaka tafi wata ƙasa kuma har wata Uku fah? Yanzu Ni kadai Zan ta zama a gida Kamar mayyah, Babu Aunty Aseey, Babu Sarfraz balle hassu" "Ko zaki bini? "Eh Allah zani" Ware ido Aayaan yayi cikin mamaki Domin abin yazo mishi a bazata, be taɓa tunanin zatace "eh" ba koda wasa. "Da gaske zaki bini?" Rufe fuska tayi tana murmushi tare da ɗaga Kanta alamun eh. "Okay naji daɗi sosai, har dai zaki je ma to gobe kawai zamu tafi tunda kinga kowa yananan be koma ba sai muyi musu Sallama kawai. Ita dai Nawaz sai bayan tace zataje ta tuna aika aikar da SARFRAZ yayi "to Yanzu idan Aayaan ya chafketa a inda babu kowa ya zatayi kenan? Duk saitaji kamar tace ta fasa binshi ma. Farin ciki a gurin Aayaan ba'a Magana, jiyakeyi Kamar ya dena tuƙin ya miƙe yayi ta rawa... Suna Isa gida bayan ya buɗe mata kofa ya nufi falour da gudu yana kwala wa mummy kira "mummy! Mummy!! Mummy!!!, Mummy kina ina? Mum ta fito daga ɗakin da su ummin Nawaz suka sauka taji Aayaan na ƙwala mata kiran mafarauta, tsaye tayi kawai tana kallonshi. "Mummy inata miki magana amma kikayi shuru, Koh So kike zuciyata ta buga? Balla mishi harara Mummyn tayi "hmmm Aayaan manya, nidai wannan washe bakin da zargadilar da kakeyi nasan ba banza ba, dole akwai wani abu, faɗamin meya faru? Kama hannunta yayi "zo muje kiji" Binshi takeyi tana mita "oh Aayaan wai kai har gobe bakasan ka girma bane? Ji yadda kake jana! "Mummy kiyi hakuri, banason kowa yaji abinda zamuce ne, saboda sirri ne. "To ai nan yayi tunda kaga mun bar inda mutane suke, yanzu faɗa min menene? "Dama Colonel ne yace gobe in shirya inje in sameshi a Abuja wai zamu wuce England akwai wani aikin ujula daya taso mana. Kanne ido Mummy tayi domin hakanan taji maganar bata gamshe taba "to Allah ya kiyaye hanya ya tsare ya kaiku lafiya yasa aje a Sa'a kuma a dawo a Sa'a" sam bata bashi damar da zaice mata zashi da Nawaz ba. Botsare fuska Aayann yayi "mummy meyasa zakice haka? "Kajimin ɗa to addu'ar danayi maka ce bakaso ko kuma wani abun nayi daban? Ni a nawa ma da zakaji shawarata kawai ka shirya kayanka yanzu kabi Aseey kaga tafiyar ma zatafi yi muku daɗi. Tsalle Aayaan yayi irin wanda yara sukeyi idan sunajin yin rigima, Wato duka plan da karyar da ya haɗa sun tashi a banza kenan! "Nifa mummy tare da sis Nawaz zamu tafi " Zaro Ido mummy tayi "lallai Aayaan akwai sauranka matar taka zaka ɗauka ka kaita filin yaƙi? "Mummy bafa yaƙi za'ayi ba, semina ce fa kawai" "Hmm to bari na faɗa maka kome za'a yi bazan baka ƴar mutane ka tafi da ita ba" Daka tsalle yayi ya dire "mummy wato nine bakyaso da kika barni nake zuwa kenan?" "Ni ina ruwana a wannan? Ra'ayin kane kaga babu abinda ya shafe ni, kuma bazan yarda insa Rayuwar ƴar mutane da aka bamu ita cikin mutunci ba a hatsari" "Mummy wallahi dakanta tace zata bini fa, kuma bari kiji. Kunna wayarshi yayi saiga muryarshi yana cewa "sweetheart inaso Nima naje England fa nanda Three days, kuma Gaskiya zan daɗe acan, Don a ƙallah zan iya kaiwa Three months" "Ya dai Madam what happened? Kasa kunne mummy tayi har zuwa inda Nawaz ɗin tace "eh Allah zani" Murmushi mum tayi domin tasamu abinda takeso, tasan yanzu Nawaz ta yarda cewa ita matar Aayaan ce, and ga Dukkan Alamu zasuba juna kulawar data dace, "to wa ya sani ma ko honey moon zasuje suke Min noƙe noƙe? Mum ta ayyana a zuciyarta. "Mummy bakice komaiba pls" "Aayann me zance illa ka ɗauke matarka ka tafi!" Ɗaga ta sama yayi tare da jujjuyata yana cewa "U Are the Best mum ever! I Love You so much, Naji daɗi da Allah yasa kece mamana. Murmushi mummy takeyi tare da cewa "saukeni Aayann kada surikata tazo ta ganni a haka inji kunya. Shima dariya yayi tare da sauketa yana cewa bari naje na shirya Don Flight ɗin safe nakeso mubi In'sha Allah, don so nakeyi gobe war haka muna chan. Nawaz Dake laɓe a gefe Duk tanajin yadda sukayi da mummyn sai taji duk kunya ta kamata, ta rasa yadda zatayi ta fito. *DON ALLAH A ƘARA MIN AFUWA NA RASHIN GANIN POSTING ƊINA DA KUKEYI AKAI AKAI, WALLAHI UZURURRUKA NE SUKAMIN YAWA, DON ALLAH ASANI A ADDU'A 🤲🤲🤲🤲🤲🤲 NAGODE"* *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *65* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Saida ta tabbatar mummy da Aayaan sun bar wajen sannan ta fito ta shige ɗakin da umminta suke zaune. Tana shiga ta faɗa jikin ummi tana haki "lallai Madina, daga zuwa saiki faɗa jikinta Kamar kin faɗa saman gado?" Cewar Ammah tana hararar Nawaz. "Ai Wallahi Ammah Bansan sanda Nawwarah zata dena yarinta tasan ta girma ba" Ammah ce tayi dariya tare da cewa "hmmm ai Madinatul munawwarah bazata dena yarintaba sai taga wani ɗan Ko ƴar a hannunki, inaga shine Kawai Abinda zaisa ta haƙura. Kunya ummin Nawaz taji, amma a cikin zuciyarta cewa tayi "Allah ka bayyanah Min mijina kila nima ina da rabon kuma ganin Wani ɗan nawa" Ita dai Nawaz duk Maganar da akeyi bata ɗaga ummin tata ba, saima daɗa lanjarewa da tayi a saman cinyarta. "Gobe War haka in'sha Allah muna gida abin mu" cewar Ammah tana samun gefen gado tana zama "Nifa Ammah nasan tsohon mijinki Kawai kika ƙosa kije ki gani" cewar Nawaz tana kanne ido ɗaya. "Eh ɗin ja'ira!! Mijin nawa nakeso naje na gani, ance muku mu irin kune da basu ɗauki miji a komai ba, saikiga mace tayi tafiya tabar miji a wata ƙasa kusan wata ɗaya wasuma har biyu... Aimu Tunda Allah yace Aljannar mu tana kasan kafarsu muka saduda muke musu biyayya, idan kema zaki yiwa kanki faɗa to gwara kiyi duk da dai Bansan Yadda kamun ludayin naku zai kasance ba. Duk sai Nawaz taji ta zargi kanta, sai take ganin kamar Ammah tasan tsakaninta da Aayaan ne shiyasa take faɗa mata wadannan maganganun. "To Ammah da kike faɗan wadannan maganganun cemiki yayi bana yi mishi abinda yakeso? "Banga alamun anayiba koda shi be faɗa minba, domin alamar ƙarfi ai tana ga mai ƙiba " Balla mata harara Nawaz tayi tareda cewa "wani mai kibar Koh? Don wani siririn yafi kwarin ƙashi" "Au Madina Rashin kunya zakiyimin saboda ina baki Shawara akan ki kula da mijinki domin ki samu Aljannah ranar gobe kiyama" Miƙewa Nawaz tayi tana karkaɗe hijabinta tare da cewa "ba'a son shawarar taki, ƴar sa eyes a abinda be shafeta ba kawai" "Yanzu Madina nice ƴar sa ayiss ɗin" kallon ummin Nawaz tayi tace "ke Rahmatu meye ayiss ɗin? Dariya ummi tayi Sannan tace "eyes yana nufin ido da Hausa". "Uwariyonki nace Madina, wato nice ƴar sa ido Koh?" Ficewa Nawaz tayi daga ɗakin gaba ɗaya tunda dama a miƙe take ... "Ƴar ƙaniya! Allah ya raka taki gona, kuma kada ki sake ki dawo ɗakin nan tunda fitsara zaki riƙa yimin" Ɗaga murya Nawaz tayi "zan gani idan ɗakin nakine da zakice kada na dawo'' Tana fita sukayi kicibis da Aayaan shima ya tawo da nufin shiga ɗakin, gani tayi ya daɗa yi mata kyau fuskarshi cike da farin ciki, idonshi har wani kyalli yakeyi, ga gashin kanshi yasha gyara haɗe da sajenshi. Murmushi yayi mata me kyau "sweetheart keda waye nake jiyoku tun ina corridor? Shagwaɓe fuska tayi "ba Ammah bace ta dameni ba" Shagwaɓar da tayi sai yaji Kamar an tsikare shi, murmushi yayi aranshi yace "mun kusa shiga duniyar da shagwaɓar zatayi Amfani" amma a fili sai yace tafiyarki zanji da ita nasan kishi ne ke damunta, kinsan tunda taga kinfita Komai shine kullum take tononki da faɗa. Dariya Nawaz tayi ta Wuce abinta tare da mamakin Kasancewar Aayaaaann soja babu abinda ya hanashi, idan yana wani abun ma bazaka taɓa cewa shi soja bane illa jikinshi da zai tona shi saboda murɗewar tayi yawa dole sai dai sojan. Shiga yayi suka cigaba da sabga dukda yana ɗan jin nauyin ummin Nawaz, "ummi Nawaz tayi muku Sallama kuwa? "Au wai dama Sallama Madina ta shigo tayi mana shine ta ɓige da yimin tijarah?" Cewar Ammah tare da kama haɓa. Murmushi Aayaan yayi "to ai Shikenan tunda bata samu tayi muku ba, nina wakilceta, dama yanzu zamu wuce Abuja ne saboda gobe zamu tafi England In'sha Allah. "Eye ɗan nan Ingila fa kace? Kai da Madina ɗinne zaku tafi Ingila? "Eh tare zamu tafi In'sha Allah" "Hmm ashe Dole tamini tijara tasan abinda ta taka, ashe tsallake Najeriya zatayi ta tafi ƙasar masu jajayen kunnuwa? Dariya Aayaan yayi " Ammah ai addu'a zakiyi mana Koh bakyaso muje ne? " Ni na isa! Allah ya kaiku Lafiya ya dawo daku lafiya, kuma Allah ya tsare ku ga dukkan sharri, yanzu zaku tafi habuja kace Koh? "Eh Ammah In'sha Allah, saboda inaso gobe mu sauka da wuri ne a England ɗin domin Akwai abubuwan da nakeso nayi, da goben zamu tafi gaba ɗaya amma sainaga bazai yiwuba" "To Shikenan Allah ya tabbatar mana da Alkhairi, kuma dai abinda zan ƙara faɗa maka shine ayita haƙuri, kasan mata akwai su da rauni, don Allah idan kaga tayi ba dai-dai ba a riƙa tsawatar mata. Sosai suka ɗan taɓa hira Sannan ya fita daga ɗakin zuwa gurin su mummy don ya faɗa mata yau yakeso su sauka a Abuja ɗin. Ita kuwa Mummy tana tare da Mummyn SARFRAZ inda suka chanza Shawara akan kada a Kawo hassu gidan, tunda har yanzu akwai sauran baƙi, abin zai iya zama na Magana, tunda dama mutane Abinda sukeso kenan. Wata innar mummy aka sa driver yakai gidan saboda ta kula da hassu ɗin. Sai bayan sun isa ta kira a waya ta tabbatarwa da Mummyn SARFRAZ ɗin cewa jikin hassu ɗin da sauƙi Sannan ne hankalin ta ya kwanta ta samu nutsuwa. Knocking ɗin Kofar Aayaan yayi, muryar Mummyn SARFRAZ ce tace "Shigo ciki" Koda Aayann ya tura ƙofar ya shiga sai mummyn tace "Au ashe ma kaine, shigo ka zauna mana" Zama yayi yana murmushi, "ya akayi ka wani zauna kana washe mana baki? "Mummy damafa nazo nace miki yanzu fa zamu Wuce abuja saboda gobe Flight ɗin safe zamubi " "Toni ina ruwana! Kawai ka ɗauki matarka ku tafi duk inda kake so kuje, na gaji da wannan zargadilar dakake yimin sai kace wani mai bikon matar datayi yaji" "Haba ke kuwa? Ya za'ayi kice haka? Aayaann kayi haƙuri kaji, Allah ya kaiku lafiya yasa aje a Sa'a, kuma ayita haƙuri da kauda kai don Allah. Murmushi Aayaan yayi domin yaji daɗin addu'ar da Mummyn sarfraz tayi mishi. Ita ma Mummyn nashi sai taji bata kyauta ba, ai ko babu komai Aayaan ɗin ya nuna kawaici da dattako tunda wata nawa amma har yanzu ya zuba ido, jifa Sarfraz jiya fa aka kai mishi yarinya amma ya kasa haƙuri. "To Aayaan Allah ya kaiku Lafiya ya dawo daku lafiya, ya bada Sa'a a Abinda zakuje yi, kuma nima dai abinda zan ƙara faɗa maka shine kada ka ɗauki Yar Mutane ka rabata da ƙasar ta ka kaita wani guri kuma kaje kana ƙuntata mata kayi tunanin Allah zai kyaleka, to wallahi kada naji kada na gani, kuma wallahi har dai ka wulakanta musu ƴa ban yafe maka ba, ina fatan dai kaji abinda nace? "Naji Mummy, kuma in'sha Allah babu abinda zai faru, zanyi iya kokarina wajen sauke nauyin ta da Allah ya ɗora Min. "To naji daɗi sosai, Allah yayi muku albarka ya baku zuri'a ɗayyiba. "Ameen mummy, mungode Allah ya saka da Alkhairi, bari naje nace ta fito sai muyi muku sallamar gaba ɗaya" Murmushi mummyn sarfraz taketayi tanajin dama Sarfraz ne haka, Amma shi ji yadda yaja mata tashin hankali daga ɗaura Aure jiya. Yana fita ya Wuce ɗakin Nawaz, be ganta ba amma yaji alamun saukar ruwa a bathroom, yasan wanka takeyi, sai kawai ya samu guri a saman side drawer ya zauna yana jiran ta fito tare da tunanin Anya ma zata yarda ta bishi yau kuwa? Befi minti biyar da zama ba sai gata ta fito ɗaure da towel pink wanda da kyar ya rufe mata mazaunai, sai wani ƙarami a hannunta tana tsane kanta dashi. Bata tsaya ako inaba sai a gaban dressing mirror, jan Kujerar tayi ta Zauna tare da ajiye towel ɗin tana ɗaukar hand dryer zata jona a socket donta busar da gashinta. Shi dai Aayaan sakin baki yayi yana Binta da kallo, be taɓa zaton kyawunta yakai haka ba, cinyoyinta da suka haɗu da hips ɗin ta suka cika towel ɗin da kirjinta daya yi bisa cikin towel ɗin yake kallo, sai fuskarta da tayi lufluf da gashi haɗe da ruwa tayi wani fresh da ita. "Hmmm lallai Allah yana sona da banyi gigin yin Aure da wuri ba, nasan da yanzu na rasa wannan. Miƙewa yayi da nufin ya ƙarasa kusa da ita donya amshi hand dryer ɗin ya taimaka mata Ita kuwa Nawaz saita yangi abu ta mudubi Kamar ya nufota, ai babu shiri ta miƙe zata zura da gudu, cikin rashin Sa'a Kujerar tayi baya, itama saita bita tare da watse wa a ƙasa. Kurma ihu tayi domin a tunaninta kila fatalwace domin firgici ma be bari ta lura cewa Aayaan bane. Da gudu Aayaan ya ƙarasa Tare Da dagota yana haɗa ta da ƙirjinshi, sorry dear I don't mean to hurt you, Bansan zaki firgita ba. Duk saiyaji babu daɗi saboda sosai jikinta ke rawa gashi har zuciyarta da ƙarfi take bugawa kamar zata fito waje. Hannunshi yasa a hankali yana kwantar mata da jiƙakken gashinta zuwa baya duk don ta samu relief, "I'm sorry pls sweetheart" Muryarta na rawa tace " babu komai, nima dai Kawai na firgita ne saboda Bansan ka shigo ba" "I'm sorry, bazan kumaba In'sha Allah, dama nazone nace ki shirya saboda yanzu zamu wuce Abuja saimu kwana acan tunda kinga Flight ɗin safe zamubi" "To bari na shirya saina fito Koh? Cewar Nawaz amma har Yanzu zuciyarta na bugawa da sauri da sauri Duk sai Aayaan yaji tausayinta ya kamashi sosai, ta zama wani so silent da ita, duk abinda yace sai tace to babu musu. "Oya to zauna na gyara Miki gashinki saiki shirya ko" namma babu Musu yaga ta zauna batace komai ba. Dryer ɗin ya kunna sannan ya fara yi mata drying a hankali, dayake ya saba yiwa Aunty Aseey da mummy ba'a wani daɗe ba ya gama, hannu yasa ya dauko straighter itama ya jona, tana kallonshi yana shafa mai yana straighting ɗin gashin. Mamaki dukya kama Nawaz, a ina ya iya duka wannan abin? Wanda wasu matan ma koda an basu basusan yanda zasuyi su kunna ba. Cewa yayi "dena mamaki" don nayi aikin daya kamata nayi miki meye na mamaki? Tana kallonshi ta mudubi yayi mata doughnut da gashin, hanyar waje yayi yana cewa "ayi kwalliya lafiya, ina falour ina jiranki ki fito" Ɗan murmushi tayi Sannan tace "to yanzu zan fito" Hakanan Aayaan yaji duk tausayinta ya kama shi, meya sauyata Lokaci ɗaya? Ita dai Nawaz yana fita ta mutstsika mai ta ɗan sa kwalli sai lip gloss, Sannan ta samu wata doguwar riga ta zira, Sannan ta zira hijab madaidaici ta fita zuwa falour. Ile kuwa a zaune ta sameshi a saman kujera riƙe da remove yana kallon Bollywood inda akeyin baghi 2 Dukawa tayi a ƙasa tace "gani yaya" Miƙewa yayi ya ɗago ta tare da cewa "wai sweet heart duk sanyin nan na menene? Nifa nafison ariƙa yimin tsiwa" Samun kanshi yayi da rungumeta gaba ɗaya a ƙirjinshi. Sannan suka wuce Dakin su ummi, cikin ikon Allah duka Anan suka samu kowa harda su Mummy. Sosai aka yiwa Nawaz faɗa kamar babu gobe, sai kuka takeyi harda majina, shi kuwa Aayaan duk yabi ya turɓune fuska wai shi an ɓata wa matarshi rai. Ana gamawa ya ciccibeta a gabansu yayi waje yana chuno baki "bamason rakiyar ma tunda da kuka za'a sallame mu, mungode, saimun dawo nan da shekara goma. "Ku Shekara dubu ma mara kunya, dama waye zai biku yaga fitsarar datafi karfinshi. Cewar mummy tana balla mishi hararar wasa, sabanin a zuciyar ta daɗi takeji tana fatan Allah yasa bazasu dawo ba sai Nawaz nada ciki Haka dai aka rabu anata raha, babu abinda Nawaz ta dauka haka ya saka ta a cikin mota shima ya shiga inda ya janyota ƙirjinshi yana ci gaba da rarrashinta. Sosai driver Dinshi ya dauki hanya dayake yau tafiyar tasu su kadai ne babu securities. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ta ɓangaren Umma kuwa zuwa Yanzu ta gama raina kanta domin ko motsa kafar ta tayi ji takeyi kamar zata mutu, ga wani uban warin ciwo da takeyi, kuma sunje asibiti har hotuna anyi amma ance ba'a ga komai ba. Sannan koda fauziyya taje Makarantar su Jamila haka tasamu Jamila ɗauke da ciki harna Tsawon wata shida, koda suka dawo gida umma ji tayi kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu. Zuwa yanzu tayi nadama yafi cikin kwando dubu, Sannan gashi a asibiti ance sai an kawo a ƙalla kusan miliyan biyar Sannan za'ayi aiki a yanke ƙafar Domin kullum abin gaba yake Dada yi. Kullum cikin kuka take tana fatan Allah ya dawo dasu Nawaz da mamanta saboda ta nemi yafiyarsu, dukta bushe ta lalace tayi baƙi kamar ba ita ba. Gashi ita tasan batada hanyar Miliyan ɗaya ma balle miliyan biyar, kuma kullum kuka takeyi da kanta tunda son duniyarta ne yasa hakan ya Faru da ita. *TO JAMA'A KUN DAI GA HALIN DA UMMA TAKE CIKI, ITA KUMA NAWAZ DA MAMAN TA KUNGA SUMA A INDA SUKE, YANZU WA GARI YA WAYA* ~*ALLAH KASA MUFI KARFIN ZUCIYARMU AMEEN*~ *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *66* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Jin jikin Nawaz ɗin yayi ya saki gaba ɗaya Sannan tanata sauke ajiyar zuciya akai-akai, kallon fuskarta dake haɗe da ƙirjinshi yayi, besan sanda wani ƙayataccen murmushi ya kufce mishi ba ganin tayi Barci peacefully abinta. Gyara mata kanta yayi domin tayi balance sosai yadda zatafi jin daɗin barcin, sosai ya tsura mata ido kamar be taɓa ganin taba, hakanan yakejin kamar an kunna pampom ƙaunarta a cikin zuciyarshi yana shatata. Azahirin Gaskiya Tunda yake a Duniya be taɓa Ganin Wata ƴa mace da take burgeshi kuma take yi mishi kwarjini lokaci dayaba sai Nawaz, yana matuƙar son ta da ƙaunar ta, ga wani Irin girmanta da yake gani. Tunda suke bata taɓa cewa ya bata wani abuba, Sannan shi ko lefe ma beyi mata ba kuma bata taɓa tambaya ba. Gashi komai kankantar abinda ya bata ta riƙa godiya kenan kamar Wadda aka biyawa Saudiyya, duka dabi'unta suna burgeshi, daɗin daɗawa kuma hakurinta da kawaici. Shiru yayi yana tunanin yadda rayuwarsu zata kasance nan da ɗan wani lokaci mara tsawo, yasan yayi sa'ar mata tako ina abu ɗaya ne yake ɗan damunshi shine tsoronshi da take nuna tanaji a fili. Kuma yasan bawai shi take tsoro ba jikinshi take tsoro, tunanin yadda zai fincike tsoron gaba ɗaya ya fara yi. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Koda Hassu ta tashi bata ko kalli inda SARFRAZ yakeba illah fara ƙwalawa Nawaz kira data fara yi "Aunty Nawaz! Aunty Nawaz!! Da sauri SARFRAZ ya miƙe ya karaso kusa da ita yana cewa "Sweet Ikraam kin tashi! Sannu, hope jikinki yayi miki sauƙi Koh? Gyada kai Kawai tayi tana zumbura baki, itafa batason taga daga ita sai shi domin gani take zai iya cewa zai kara hake mata. "Ina Aunty Nawaz ɗin take?" "Ta tafi amma mummy ta turo inna zuwairah ta ci-gaba da kula dake" A hankali ta mike da nufin fita falour amma saitaji kafafuwanta sunyi mata tsami "koma ki zauna bari na turo Miki ita" yana gama faɗar haka yasa Kai ya fice daga bedroom ɗin. Ba'a fi minti uku ba saiga inna zuwairah ta shigo fuskarta ɗauke da matsakaicin murmushi "ƴa ta Ashe kin tashi? Ya jikin naki? Sosai Hassu taga yanayin matar yayi mata saboda dama ranar biki ma tanata nan nan da ita har zip ɗin rigarta ta gyara mata. Murmushin itama tayi Tare Da cewa "da sauƙi inna" "Yauwa ƴar Albarka! Yanzu bari na haɗa miki ruwan dumi sai ki ƙara gasa jikinki kiyi wanka saboda inaso kisha magungunanki yadda zakiji sauƙi da wuri In'sha Allah" "To inna Nagode sosai" cewar hassu tana ɗan duƙar dakai, ga Dukkan Alamu dai babu Aunty Nawaz a cikin gidan, kenan sunje sun faɗawa mum abinda ya faru kenan. Ajiyar zuciya ta sauke tare da girgiza kai "wallahi koma menene bazanga laifin kowa ba, yaya Sarfraz shine silar komi" Lafiyayyen ruwa inna zuwairah ta haɗa mata Wanda yasha kayan kamshin jiki da gishiri, sosai taji daɗin ruwan fiye da Wanda Nawaz ta haɗa mata (Ni dai nace ai Nawaz ɗinma tayi ƙokari tunda bata taɓa tsintar kanta a irin haka ba) Saida ta chanza mata sau biyu sannan ta haɗa mata Wanda zatayi wanka normal, ko bayan ta shirya sai takejinta har wani karfi ne ya ƙaru a jikinta da Lafiya. Magungunan ta inna ta kawo mata tare da madara da abincin da Nawaz ta dafa ɗazu, sosai hassu taci abincin Domin yanzu taste ɗin bakinta ya dawo, madarar tasha Sannan ta kora magungunan nata. Wata roba Inna zuwairah ta miƙo mata tace "shanye wannan ma" Tsaff hassu ta gane menene daga ganin robar tasan cikin kayan da suka tawo dasu daga sudan ne sanda sukaje gidan Aunty khatoume gyaran jiki. Babu musu ta amsa ta shanye dayake kusan ko wanne Akwai zaƙi. Ba'a ɗauki lokaciba suka saba da inna zuwairah sosai saboda itama akwai son yara mata gashi duka ƴaƴanta mazane babu mace ko Guda ɗaya. Shi dama Sarfraz tuni ya kama kanshi yabar gidan domin yasan inna zuwairah bata ɗaukar raini sam saboda danta na biyu sa'an shine yasha yaje ya tarar tana cin ubanshi idan yayi mata laifi. Anyi mata Auren wuri dayake ba'a cikin maraya suka tasoba, amma cikin ikon Allah sai Allah ya buda wa mijinta ya fito dasu cikin gari, tundaga nan zumunci mai ƙarfi ya ƙullu tsakanin mummyn Sarfraz da ita. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Basu suka kai Abuja ba sai cikin dare, a Sheraton hotel suka sauka Saboda dama tun Kafin su ƙarasa yasa akayi mishi booking ɗin ɗaki, V.I.P part aka kama mishi, babba ne sosai kuma tsarinshi dole ya burge ka duk kuwa iya gwale abinka. A kame Nawaz ta zauna a saman light Blue ɗin sofa data zagaye ɗakin, jinta takeyi kamar tayi wani babban laifi a rayuwarta, tunani ta fara "yanzu wai ni shikenan babuni babu kuma zama da ummina Kamar yadda muke ada? yanzu yaya Aayaann shine dolena? Dashi zan rayu? Idan banyi mishi biyayya ba nan ma Allah zai yi fushi dani? Ji tayi jikinta yayi sanyi ƙalau Sannan ta rasa duk wani courage nata, take zuciyarta ta sallama komai ta aminta da kaddarar data sa suka haɗu da Aayaan har Gashi a yanzu ya zame mata miji. "Sweetheart tashi ki shiga kiyi wanka, na haɗa miki ruwa me ɗumi nasan zakiji daɗin shi sosai" maganar Aayaan kenan Wadda tasa Nawaz dawowa cikin hayyacinta da sauri. "Yaya aini ya kamata na haɗa maka ruwan wanka bakai ka haɗa min ba" "Kefa Sarauniya ce a cikin faɗar zuciya ta, babu abinda bazan iya yi miki ba muddin befi ƙarfina ba, hope banyi laifi ba dana haɗa ba Tare Da na tambayi mai girma Sarauniya ba? Ware idanunta tayi "yaya bazakayi min laifi ba, Nagode sosai! Bari na shiga nayi" da sauri ta miƙe Tare Da bin Hanyar dataga ya fito. Zama Aayaan yayi a dai-dai saitin inda Nawaz ta tashi, ɗumin jikinta be bar sofa ɗin ba sanda ya zauna "me yake Yawan sa sweetheart tunani ne? Ina Fatan bani nake takura mata ba! Inajin tsoron addu'ar da mummy tayi na cewa Idan na Cutar da ita bazata yafe min ba, but bari ta fito in tambayeta meke damun ta" Shiru shiru kusan awa ɗaya Nawaz taki fitowa Daga bayin, shi kanshi yanaso ya watsa Ruwan kafin ya kwanta, gashi harya fara gyangyadi saboda gaba ɗaya a gajiye yake tuɓus. Bakin bayin ya ƙarasa ya fara kiran sunanta, amma shiru babu amsa, ƙara ƙarfin kiran yayi namma shiru bata amsa ba, wata irin fargaba ce ta kamashi Lokaci guda ya tura bayin da ƙarfi. A cikin bath ya ganta ɗaure da ɗan ƙaramin towel ta ɗuƙunƙune jikin ta guri ɗaya tanata sharar barci, kasaƙe yayi yana kallon yadda take barci kamar Wadda take akan gado, dariya sosai abin ya bashi don yasan kunyace ta hanata fitowa. Duƙawa yayi ya ɗauketa dukanta tare da fita daga bayin zuwa cikin bedroom, a Saman King size bed ɗin ya kwantar da ita sannan yasa duvet ya rufeta. Bathroom ɗin ya koma tare da haɗawa kanshi nashi Ruwan wankan, kamar mace haka ya zauna yana ƙalƙale-ƙalƙale, ko ina saiya wankeshi daban kuma a tsanaki. Koda ya gama wankan shima be wani tsaya saka kaya ko shafa Mai ba, towel kawai ya ɗaura a ƙugunshi Sannan ya haye saman gadon tare da janyo Nawaz Zuwa ƙirjinshi yana rungumeta sosai sannan yaja duvet ɗin ya rufesu. Dayake barcin ya gama kama mishi ido sosai, ko minti biyar ba'a yi ba sai jin saukar numfashi nayi yana sauka peacefully. Sai wajen ƙarfe Uku Nawaz ta farka, jinta tayi cikin Wani faffaɗa, yalwatacce kuma Ni'imtaccen ƙirji, to bata tsaya wani dogon tunaniba tasan Aayaan ne, sosai yanayin ɗumin jikinshi ya kayatar da ita saboda duk uban sanyin da ake yi sam ita bataji, har wani damshi-damshin zufa ne ma yake a tsakanin kirjinsu daya haɗu guri ɗaya, a hankali ta buɗe idonta kamar Me jin tsoron buɗewa. A saman fuskar Aayaan ta sauke idonta, Zuba mishi idanunta tayi tana ƙare mishi kallon da bata taɓa yi mishi Irin Shiba, sosai taga kyawunshi wanda bata taɓa ganin irinshiba dayake dakin gauraye yake da wadataccen haske. Zarazaran gashin idonshi taketa kallo kamar wanda yasa fake lashes, Saida ta kalla ta gaji Sannan ta dawo kan hancinshi, Gaza haƙuri tayi Saida tasa hannu ta taɓa hancin, tunda take bata taɓa ganin hancin da yayiwa meshi kyauba Kamar nashi, sosai ya zauna a tsakiyar fuskarsa gashi dogo and well pointed. Babu abinda ma ya tafi da imaninta kamar laɓɓansa yadda suke pink-pink maroon-maroon brown-brown kamar wanda ya shafa wani jan baki na musamman, sosai ta shagala wajen kallonsu, shape ɗin su kanshi abin kallo ne ga wani kwantaccen gashi me santsi a saman top lip ɗin. Yatsanta manuniya tasa ta taɓa leɓen, hakanan taji jikinta yayi mata wani iri, taushi sosai taji saman laɓɓan nasa, murmushi ne ya suɓuce mata sannan afili tace "taɓ wannan mutumin da Mace ce Bansan Irin goslow ɗin Da za'a riƙa yi a kofar gidan suba, jifa kyau kamar danshi aka halicci Kowane abu mekyau" "Ai ban kaiki kyau ba my Queen👸" Koda wasa Nawaz bata taɓa zaton idonshi biyu ba, ruɗewa tayi gaba ɗaya kunya ta rufeta, ji tayi dama ƙasa ta buɗe ta rufta da ita kawai ta huta da wannan abin kunyar data tafka, ita mema ya Kaita yin wannan ɓaranɓaramar? "To kici gaba, yanzu saura gira ki duba kiga itama tayi Miki ko akwai gyara, and daga gira sai gashin kaina da kunne, idan kika kainan kin gama da kai sai kuma a koma kirji. Sai hannu da yatsu, infact har manhood ɗina ma saikin duba kinga ko ya miki! "Yanajin yadda bugun zuciyarta ya ƙaru, dariya yakeso yayi amma bayaso ta fahimci wasa yake mata, to sweetheart kici gaba mana! Tuni Nawaz ta ɗauke numfashinta, kunya nauyi da tsoro ne suka saukar mata lokaci guda jin cewa wai har length Dinshi saita duba. Bata taɓa zaton wasa yakeyiba saboda yadda taji muryarshi a dake. "Shikenan tunda ke bazaki yabi ɗan mummunan mijin naki ba, Ni bari na faɗa miki abinda yaja ra'ayi na akanki my beautiful wife" "Kinga da fari babu abinda ya fara ɗaukar hankalina akanki kamar jarumtar da kikayi a daren da kika gudo daga Wajen ƴan ta'addan nan. Na biyu kuma yadda kika damu da wanda kuka tawo tare dashi (SARFRAZ) kinga hakan yana nuna kinada riƙon Alkawari kenan. Na uku yadda ƙaddara tasa kika zauna tare damu Batare da kin shirya ba, naga ko dai-dai da rana ɗaya baki taɓa nuna kin damu ba duk da baki sammu ba, kin yarda kin zauna damu koda a cikin ranki bakya so, hakan ne ya nunamin kinada amsar kaddara, kuma koda Mutum ya aureki wani abu ya faru daga Baya nasan bazaki guje mishi ba. Na huɗu shine yadda kika ɗauki mummy kamar Wadda ta haifeki, kullum cikin girmama ta kike da mutuntata, sannan Aunty Aseey ma kin ɗauketa kamar yayarki babu raini ko nuna damuwa tsananin ku, Sannan muhsien ma kin daukeshi kamar ɗan da ke kika haifa, sam Bakya gajiya da shirmenshi. Kinga ko iya nan na tsaya nasan na haɗa qualities ɗin da akeso mace tagari ta samu, balle Akwai saura babu adadi Kuma Kinga duk sanda zan taɓaki sai kince min babu kyau, to wallahi Allah ne kadai yasan irin daɗin da nakeji a cikin zuciyata. Sannan abu kaɗan zaki kawo aya ko hadisi. Idan nace zan iya lissafa miki abubuwan da suka jani zuwa gareki wallahi nayi ƙarya. Kinga kinada kunya, kuma duk inda kikaga kunya to akwai imani a gurin Domin tagwayen junane ɗaya baya tafiya saida ɗaya. Ga hakuri ga kawaici da yakana, hmm nifa na dace, Allah ya zaɓeni cikin miliyoyi kuma babu abinda zan iya yi mishi sai godiya gareshi a kullum. Yanzu abar fannin halayyah a dawo dabi'a. A yadda na lura da dabi'un ki shine Bakya wasa da Sallah, kinada son addinin ki sosai, nasha Kamaki kina karatun Alqur'ani mai girma, kuma gaskiya zaki fadeta koda ke bazata yi miki daɗi ba. Nanma zan barshi haka. Ƙirar jiki kuwa Bansan me zance ba gaskiya, Domin kedin full package ce, sama da ƙasa dass, komai yaji babu makusa daga body structure har kyawun fuska. Donma dai har yanzu ni ɗin an ɗaukeni a Matsayin dodo kinki bani damar dazan gama mallaka miki kaina gaba ɗaya. Zuwa wannan lokacin babu abinda jikin Nawaz Keyi in banda rawa, haƙiƙa idan tace bataji daɗin yabon da Aayaan yayi mata ba tayi karya, amma kalmomin da yayi Amfani dasu ne sunyi mata Nauyi. Sosai Aayaann yakejin dama su dauwama a yanayin da suke ciki har abada, ya gama karantar cewa Nawaz ta afka cikin soyayyar shi batare da itama ta sani ba, Yanzu abu ɗaya ne ya rage mishi da zai yi yaƙi dashi shine kunyarshi da take matuƙar ji, ya lura kunyar cema take kawo tsoron. Daɗa rungumeta yayi sosai a ƙirjinshi tare da sumbatar goshinta yana cewa "my fear fear wife" A haka har barci ya ɗaukesu gaba ɗaya, koda asbah ma ya rigata tashi, shiga bathroom yayi yai wanka Sannan ya haɗa mata nata ruwan Sannan ya fito ya tasheta a hankali "sweetheart kije kiyi wanka kizo muyi Sallah sai mu shirya, kinsan 6:30am jirginmu zai tashi Koh? Harta yunkura zata tashi saita tuna da abinda ya Faru jiya da dare, sosai ta koma ta lafe tare da cewa "to ka tafi Zan tashi" Murmushi yayi donya gane abinda ta tuna " as you say my Queen" matsawa yayi gefe sannan ya juya bayanshi yadda koda ma taganshi bazataji kunya ba. Salalau jiki a mace haka ta miƙe ta shiga bayin kamar wadda babu laka ajikin ta tare da turo ƙofar tana murmushi. Ko Bayan ta shiga shima Aayaan murmushi yayi Domin childish behavior ɗinta na matukar burgeshi. Ta daɗe da gama wankan amma ta kasa fitowa, duk towel ɗin dake cikin bayin ƴan ƙananu ne sosai, gashi kuma ita gaskiya bazata iya fitowa gaban Aayann a haka ba. Aayaann na tsaye harya fara gajiya, sanin cewa ba fitowar zatayiba yasa shi tura kofar bayin tare da ciccibarta yana fitowa. Jikinta taketa karewa wai ita a dole kunyarshi takeji, shammatarta yayi ya fige towel ɗin daga jikinta gaba ɗaya, aiko babu shiri takai mishi wata wawiyar runguma tare da fashewa da kuka tana cewa "don Allah yaya ka bari, kayi hakuri". "Ni bakiyimin laifi ba mai nakeso na shafa miki saina shirya ki saboda kinsa mun kusa makara. *Fatan alkhairi ga kowa* *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *67* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Kuka sosai Nawaz ta fashe mishi dashi akan don Allah ya kyaleta kada ya shafa mata zata shafa da kanta. Sosai abin yake ƙayatar da Aayaan domin dama Allah ya halicce shi dason mace mai tsoro da kuma ƙarfin hali a wani fannin, kuma Nawaz duk tana dasu. Duƙawa yayi ya ɗauki towel ɗin a inda ya faɗi sannan ya rufa mata a bayanta, ajiyeta yayi a saman gado tare da cewa "bari nayi mana order ɗin abinda zamuyi break fast kafin mu tafi, and kuma ki tabbatar kinyi sauri kin shirya kafin in dawo, don inba haka ba saina shirya ki da kaina. Yana fita ta miƙe da sauri ta ɗauki doguwar rigarta ta zira, ko bra ɗin ma saita ƙasa tasata, mai taɗan mutstsika agaggauce sannan ta maida hijab ɗinta, ai kuwa tana gamawa saiga shi ya shigo riƙe da take away guda uku, wata budurwa na biye dashi da flask da disposable cups a hannun ta. A saman table ta ajiye Sannan ta fice, shikuwa gabanta ya ƙarasa yana cewa ''Sweetheart anya wannan shirin na Allah da Annabi ne kuwa? Fitata ace har kin gama shiryawa" Murmushi dai kawai tayi mishi don bata da tacewa kuma baso take zancen nasu yayi tsawo ba. "Zo ki zaɓi abinda kikeso Anan" "Ko wanne ma kabani inaso" cewar Nawaz a hankali "Nop Gaskiya saikin zaɓa! if not kuma na baki da kaina" Gabanshi ta dawo tare da buɗe duka take away ɗin, farfesun kaza ne a cikin ta farko, ta biyu kuma farfesun naman rago na ƙarshen data buɗe nema taga snacks ne marasa nauyi. Shi ta riƙe tare da cewa "wannan nakeso" Murmushi Aayaan yayi domin dama yasan bazai wuce shi zata zaɓa ba "to ai nima shi nakeso" Miƙa mishi tayi tare da cewa "gashi Ni bari na ɗauki kazan kawai" "Nop sai dai mu raba gaskiya" ita dai Nawaz shiru tayi tana binshi da ido domin ta gane neman magana kawai yakeyi. Tana kallo ya ɗauki Flask ɗin Tare Da tsiyaya musu mint tea a cikin cups ɗin sannan ya ajiye mata a gaban ta, take away ɗin ya ajiye a tsakiyarsu tare da cewa "to Bismillah muci" Batason ta riƙa yawan yi mishi musu domin ta lura kamar hakan yakeso, domin tana farawa sun soma yin jayayyah kenan. Kallonta yakeyi ta gefen ido yadda take yafitar cake ɗin kamar ana yi mata dole, tea ɗin ma idan tayi sipping Dinshi saita jima bata kuma kaishi baki ba. Take away ɗin da kazar take ciki ta janyo tare da buɗewa, cinya ɗaya ta ɗauka takai bakinta ta gutsura a hankali, sosai tayi mata daɗi yadda taste ɗin be Wuce ƙa'ida ba saboda sosai kamai yayi normal. Tama manta da wani Aayann na gurin saida ta cinye cinya guda biyu ta ɗauki ƙirji Sannan ta tuna, basarwa tayi ta ɗan yagi kaɗan sannan a ajiye ragowar tana miƙewa. Bathroom ta shiga ta wanke hannunta tare da kuskure bakinta Sannan ta ɗauki towel ta goge. Tana fitowa shima ya shiga, haka dai kowa yayi jugum kamar kurame, wayarshi ya ciro tare da sanar da driver yayi warming ɗin mota gasunan fitowa. Komawa yayi kusa da Ita ya zauna sannan yace "my beloved Hope Ban ɓata miki rai ba, naga kamar kina fushi dani". Babu shiri tayi murmushi "Wallahi Babu abinda kayi min, kawai dai Bansan me zance maka bane shiyasa kaga nayi shiru. "Thank God tunda sarauniyata ba fushi takeyi daniba, amma da harna tsorata " Dole yasa ta ƙarayin murmushi duba da yadda yayi maganar kamar gaske. "Let get going, driver is waiting" Miƙewa Nawaz tayi tare da duƙawa tana zira takalmanta sau ciki, shima Nashi ya zira yana kallonta yana taɓe baki. Cewa tayi "menene?" "Kawai dai Naji muna tsami ne, kinsan kayan jiya muka mayar, kuma gaskiya banaso mu shiga jirgi aji muna wari saboda raina mana class za'a yi. Da sauri ta ƙarasa gabanshi tana shinshina ƙirjinshi "yaya wallahi kamshi kakeyi sosai, kamshin ma me daɗi " Rau rau Aayaan yayi da ido "Nasan tunda kikace haka Allah tsami nakeyi " "Wallahi kamshi kakeyi me daɗi sosai" Kashe mata ido yayi "dagaske" ɗaga kai tayi "eh da gaske" Be jira Komai ba ya rungumeta a ƙirjinshi tare da kama bakinta yana bata 2minute kiss "gaskiya sweetheart inaga sai munje kasuwa na siyo Miki wayau don sam bakyada wayau ko kaɗan" Ita dai Nawaz rufe ido tayi Domin tun kiss ɗin da yayi mata kunya ta rufeta. Ciccibarta yayi suka fita daga ɗakin, betsaya ko rufe kofar ba ya ƙarasa reception ya basu key ɗin Tare Da cewa suje su gyara dakin kuma su rufe. Duk Abin Nan da akeyi Nawaz na rungume a ƙirjinshi, ko a cikin mota kanainayeta yayi, sanda suka isa airport ɗin ma be bari ta taka da kanta ba, nan ma shi ya ciccibeta, duk abin duniya ya ishe ta, ga wata uwar kunya dake damunta. Saida yayi clearing ɗin komai Sannan sukayi Sallama da driver akan zaiyi ƙoƙari ya koma Zaria yau saboda a Wuce Maiduguri Tare dashi. VIP nanma suka sauka, a seat ɗinta ya ɗora ta sannan yasa mata belt, ita kuwa rufe idonta tayi Kamar me barci saboda wata uwar kunya data kulluɓeta. "Zama ki buɗe ido ne idan kikaji bakina cikin naki" Ai kam da sauri ta buɗe saboda tasan tsaff ze iya aikata Abinda yayi ikirarin yi, sai dai sam taƙi yarda su haɗa ido dashi. Gyara belt dinshi yakeyi Amma idonshi na kanta, ya lura akwai tsoro tattare da ita sai dai tayi ƙoƙarin basarwa. "Sweetheart what's wrong?" Jinjina kai tayi Sannan tace "Nothing kawai dai harna Fara kewar ƙasata ne tun Kafin in barta. Murmushi Aayaan yayi "you're right dear, Allah dai ya kaimu lafiya kuma ya dawo damu lafiya" "Ameen" Nawaz tace tana satar kallonshi, ai Kuwa charaf suka hada Ido, take ya sakin mata wani shu'umin murmushi me ɗauke da fassara kala-kala. Saurin kawar da kanta tayi itama tana murmushi ƙasa-ƙasa. "Saura ƙiris dai" cewar Aayaan yana kashe mata ido ɗaya Maida Idonta tayi ta rufe tana sauraron bugun zuciyarta, saboda gaba ɗaya tsoro ne ya kamata amma tana ƙoƙarin dannewa saboda kada Aayaan ya samu abinda zai riƙa tsokanarta nan gaba, sarai Aayaan yasan bata taɓa hawa jirgi ba, ya kyaleta ne don yaga iya ƙarfin jarumtarta. Haka aka fara sanarwa cewa "All passengers should please fasten their seatbelt" Su dai dama tuni sunsa nasu belt ɗin kawai Sai sukayi shiru suna sauraron motsin kowa. Kara rufe ido Nawaz tayi tana addu'a a cikin ranta, duk abinda take yi Aayaann yana kallonta, sosai jarumtarta ta ƙara burgeshi "Lallai kin amsa sunan ki na matar soldier, bari ma mu gama sabawa har harbi zan koya miki saboda koda ta kwana" shi kaɗai yake hira da zuciyarshi Sosai ya shiga tunani akan rayuwarshi da Nawaz, tunda yake be taɓa kawowa kanshi Aure nan kusa ba, kuma be taɓa tunanin akwai wadda zata chanza mishi ra'ayi cikin sauƙi hakaba, ya ajiye cewa Allah subhanahu wata'ala ne Kawai ya kawo mishi Nawaz a Matsayin mata ba Tare Da wata dabara ko wayau nashiba. Kuma zai cigaba dayi mishi godiya har ƙarshen rayuwarshi.... Firgigit ya dawo daga nisan tunanin da yayi, hannu yasa ya taɓa kafaɗarta donya ce mata ta buɗe idonta sun dai-dai ta a sama, amma cikin Sa'a sai ya Tarar Ashe tayi barci. Murmushi yayi yana kallon kyakkyawar fuskarta sannan cikin zuciyarshi yana jin wani abu mai ƙarfi game da ita, dramar jiya da dare ne ta dawo mishi, sanda Nawaz ta daddage ta zuba mishi ido tana ƙarewa halittar shi tanadi batasan tun tashinta shima ya tashiba, duk Abinda tayi yana jinta kuma shi hakan ma daɗi yayi mishi yadda ya lura halittar shi tayi Mata. Har yau ya kasa yarda cewa shekarar Nawaz 25, Ganin yarinta yakeyi ƙuru-ƙuru a duka lamuranta, shi a nashi gani yakeyi idan tayi wutar gaske to ƙila ace 20years. Lumshe ido yayi ba wai don yana jin barci ba kuma ba wai don ya gaji ba, sai don wani irin ɗoki dayaji yana kamashi, haƙiƙa yana son soyayya kuma yanaso ya maida matarshi Tamkar ƙawa a gare shi, yanaso suyi sabon da babu wani abu dai-dai da girman ƙwayar zarrah da zasu iya boyewa junansu. Kuma ga Dukkan Alamu ya fara Ganin alamun Nasara, saboda ya lura cewa zuciyar Nawaz ɗin wanke take tass babu kowa a ciki, yanzu ɗora hadda ne Kawai ya rage mishi, tunanin mafita ya fara yi. Ai kuwa beyi nisa ba Allah ya taimake shi ya samu, jinjina kai yayi yana daɗa jajdada wa kanshi cewa tabbas mafitar tayi. Waya ya ciro a aljihunshi ya fara rubutu a cikin notes yana saving saboda beso ya manta, still kuma yana so ya turawa haidar sako Amma babu dama saboda ya rigada yasa wayar a Flight mode. Ajiye wayar yayi a saman cinyarshi yasa hannu yana gyara mata kanta, saboda ya ɗan karkace kuma beso yayi mata tsami, haɗa ido yayi da wata baturiya ta sakar mishi murmushi alamun ya birgeta "couple's?" Baturiyar ta tambaya "Yea" cewar Aayann. Wani murmushin ta ƙara yi tare da cewa "wish u All The Best" "Ameen thanks" Aayaan yace yana murmushi, sosai yaji daɗin addu'ar datayi musu koda kasancewarta ba musulma ba. Attendant ce ta fara zuwa tana tambayar su me za'a kawo musu, wasu suce ruwa wasu su faɗi wani Abu daban, data zo kan Aayaan sai yace mata he's Okay Amma idan Madam Dinshi ta tashi zai nemeta. Dariya tayi tace "okay I will always be ready" Jinjina kai yayi alamun ya gamsu... Duk second ɗaya idonshi na kanta, ya rasa me yasa yakejin kamar ya buɗe cikinshi ya sakata ya huta, wata irin ƙauna yakeyi mata wadda besan sanda ya soma ba, yanajin kamar idan babu ita bazai iya rayuwa ba. Duk tsawon tafiyar amma sai Aayaann yaga kamar ƙiftawa da Bismillah har an fara sanarwa cewa "kowa ya shirya sun iso kuma jirgi na gaf da sauka, abinda be lura dashiba shine tun Kusan 35minutes baya Nawaz ta tashi Amma kunya da tsoro ya hanata ta nuna idonta biyu. Bayan jirgi ya dai-dai ta a ƙasa aka buɗe kofa passengers suka fara fita a jere a jere, Aayaann ne ya miƙe da nufin ya ciccibi Nawaz Bayan ya cire mata seat belt ɗin, buɗe idonta tayi da sauri tare da cewa "yaya ka barni zan iya" Mamaki ne ya kama Aayaan Yadda yaga idon Nawaz tarwai babu alamun barci "kenan rainamin wayau kikayi dama idonki biyu Koh?" Ciccibarta yayi batare daya kula taba, Ita kuma ta fara wuntsil-wuntsil wai ya sauketa zata iya. Yana sauka daga step ɗin jirgin amma idon kowa na kanshi, ganin irin kallon da Turawan keyi Musu yasa Nawaz ta natsu ta dena wuntsil wuntsil din tare da rufe idonta, "Sweetheart kici gaba mana" "Baka gani kaja mana kallo" "Idan har kikaga abu yaja hankalin bature to tabbas ya burge shine, don haka sha'awa muka basu shiyasa suke kallon mu" "Ni dai yaya Aayaann don Allah ka sauke Ni" Be kuma kulata ba har saida ya dangana da inda taxi 🚕 suke a jere, buɗewa yayi ya sakata sannan shima ya shiga, drivern ne yace "sir where will i head to?" "Royale Shire hotel" abinda Aayaan yace mishi kenan a takaice, "yaya wai nikam wace iriyar tafiya mukayi ne? Babu komai fa sai kayan jikinmu kamar wasu Yan gudun hijira" "Bazaki gane bane, koda mun tawo da kayan ba lallai su sawun miki Anan ƙasar ba, kinsan ba irin shigar mu dayaba, zamuje boutique ki zaɓi waɗanda kikeso Ni dama inada kaya a ɗakina" Gyada kai kawai Nawaz tayi tana bin cikin garin da kallo ta window ɗin dake gefenta "garin yayi Miki?" "Yea sosai, sai naga yawancin abubuwansu kamar yana alakanta sarauta" "Yea haka garin yake sai ma kinje beckingham shine zakiyi kallo har ki gaji" Murmushi Nawaz take tayi, a Cikin zuciyarta tana mamakin wai yau dalilin Aure itace a England, Lallai komai yanada nashi Dalilin" Sunyi tafiyar aƙalla minti 25 drivern yayi Parking a dai dai wani damfareren hotel, babba ne sosai don a ƙalla yakai hawa 30 kuma faɗin shi ma zai kai unguwa guda, mutane ne keta kai komo, wasu suna fita wasu suna shiga, daga yadda zakaga mutanen kasan ba zallar Yan kasar bane, don wasu farare wasu jajaye wasu yellowish fari wasu kuma baƙaƙe, wasu chocolate. masu saye da siyarwa ne keta cinikayyah a bakin hotel ɗin, don gaba ɗaya gaban hotel ɗin shaguna ne, wasu na ƴan kunne, wasu kayan sawa wasu takalma da jaka wasu kuma store ne na kayan maƙulashe. Baza Ido Nawaz tayi tana kallon iKon Allah, lallai Allah ɗaya gari banban, idan kana wani gurin sai kaga kamar babu wasu illah ku kadai, amma ji ikon Allah wata nahiyar duniyar suke kuma kowa yanata tashi sabgar. Kama hannunta yayi suka shiga cikin wata babbar hanya sannan yabi hannun dama inda ya danna button ɗin lifter, ƙofar ce ta buɗe suka shiga ciki Sannan ta koma ta rufe, 17 floor ya danna, ita dai Nawaz tana tsaye tana kallon ikon Allah. Bata Ankara ba taji ya fincikota ta fado ƙirjin shi, "Sweetheart wannan shine mafarin Rayuwar soyayyar mu, anan zamu gina ƙauna da amana, inaso ki ɗaukeni a matsayin dan uwanki, kaninki, yayanki, malaminki, babanki, abokinki, mijinki, abokin wasa, abokin karatu, masoyi, abin kauna, garkuwa kuma ginshikin ki, ina ƙaunarki sosai *Madinatul munawwarah* kuma ina fatan zamu rayu cikin ƙauna da aminci. Shiru Nawaz tayi tana sauraron bugun zuciyarshi, tabbas ta tabbatar da wannan maganar daga can Cikin tsakiyar zuciyarshi take fitowa kuma tabbas tayi na'am da soyayyar da Aayaan yake yi mata, kuma a yanzu ta fara tuhumar kanta meyasa bazata zage itama ta nunawa me ƙaunarta ƙauna ba?. Lifter ɗin ce ta tsaya Sannan ƙofar ta buɗe, a yanda take a rungume a ƙirjinshi haka suka fita zuwa cikin harabar ɗakunan, bakin wata ƙofa taga ya tsaya, a jikin kofar an rubuta *Room 315* card ya ciro yayi swapping ɗin shi a jikin wani sensor aikuwa take ƙofar ta buɗe, direct ya shiga da ita ciki, wani babban royal falour ne babba sosai, ita dai Nawaz raba idanuwa take tayi tana mamakin abubuwan da take tacin karo dasu tunda suka sauka a garin. Ɗakin tsaff yake, har kamshin rurare ne da air freshener Suke tashi, kuma ko kaɗan babu ƙura Kamar wani na zaune a Cikin ɗakin. Direta yayi a saman wani tintin da akayishi da zallar katifa yana cewa "welcome to the royal home of Love, kinga tunda kika shigo gidan nan Shikenan babu ke babu kuma jin kunya ta, domin mun riga mun zama abu ɗaya, tare zamu riƙa yin komai, kamar su girki, wanka, ke Komai ma. Kirjintane ya bada dararam, ai kuwa Aayaan ya ɗage gira Tare da cewa "bari naje na haɗa mana ruwan wanka sai inzo muje muyu ko? Ita dai Nawaz na zaune Kamar gunki tana duba yadda abubuwan da Aayaan ya lissafa zasu yiwu. *Don Allah a ƙara yi min afuwa na Rashin jina da kukeyi na kwana biyu, ina fatan kowa yana Lafiya* *MATAR RASHEED* ✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *68* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Tayi nisa cikin tunanin har yaje ya haɗa ruwan wankan ya dawo, bata ankara ba sai ji tayi ya sureta yayi corridor ɗin bayin da ita. "Don Allah Don Annabi ka taimaka ka saukeni kaga ko Kayan ban cire ba, kuma Allah zanyi da kaina...." "Nop bazan bari ba, meye amfanina? Duk zanyi Miki da kaina fiye da yadda ma ke zakiyi" "Wayyo don Allah kayi haƙuri yaya!" Dariya Aayaan yayi "gaskiya bazan iya hakuri ba, kuma as from today Nayi cancel ɗin yaya, dole kice Aayaan ko kuma ki samin wani sunan na daban. Rigar jikinta yake ƙoƙarin cirewa ita kuma ta fara ƙankame jikinta tana girgiza kai "yaya kunya nakeji wallahi, don Allah ka taimakeni ka kyaleni!" Ko bi takanta beyiba ya cire rigar, itakam saita rufe idonta gam kamar wadda taga dodo, tanaji ya cire mata sauran Kayan jikinta duka babu yadda ta iya. Ƴan seconds taji shiru Alamun yana cire nashi kayan, ai kuwa sai jinta tayi tinjim ya ɗauketa duka sun afka cikin jacuzzi ɗin daya haɗa ruwan wankan, duk tabi ta ƙanƙame kamar wadda ruwan sama yayiwa dukan tsiya da daddare, jikinta har rawa yake yi. Duk yana ankare da ita amma ko a jikinshi domin yasan idan ya biye mata babu ranar da zasu zama ma'aurata na haƙiƙa. Ita ya fara yiwa wankan sannan shima yayi, towel guda biyu ya ciro a towel rack, ita ya fara lulluɓewa sannan ya ɗaura nashi a ƙugun shi. Cicciɓarta yayi suka koma bedroom ɗin, tanajinshi har ya gama shafa mata mai yasa mata kayan da batasan wane kala bane domin har zuwa yanzu ta kasa buɗe idonta. Ji tayi ya ɗauketa ya ɗora ta a saman kujera, nan taji ƙarar hand dryer, gyara mata gashinta yayi sosai, sannan yayi Parking ɗinshi in a messy bun. Maida ita yayi ya zaunar a gefen gadon Sannan taji alamun shima yana shiryawa. Zuwa ten minutes taji ya kuma cicciɓarta, tsaida ita yayi akan kafarta sannan yace "soulmate pls open your eyes and rate my work" Yanda kasan gunki haka Nawaz ta koma domin ko motsi ƙwaƙwara ta kasa "pls my reality nace ki buɗe idonki ki ba aikina marki" Nan ma dai Nawaz tsit tayi babu respond "Okay tunda bazaki buɗe idonba bari nayi mai gaba ɗayan danasan kinajin tsoro, sai inga me zakiyi, Ni dama wallahi daurewa kawai nakeyi san....... Ai bata bari ya ƙarasa maganar dayayi niyar yiba ta buɗe idonta amma ƙasa-ƙasa, dariya ce ta suɓuce wa Aayaan be shirya ba "wai itakam wannan wace irin tsana tayiwa Mu'amular Auratayyah ne? Ace zata iya yin komai idan aka yi mata barazana da shi" Koda Nawaz ta buɗe ido ganinsu tayi tsaye gaban standing mirror, sanye take da wata designer ɗin doguwar riga Pink anyi mata spachs da ɗigo ɗigon baƙi. Shima yasa NORMAL T-SHIRT Pink me V neck sai baƙin wando chinoz. Sosai taga sunyi wani irin masifar kyau da matching, gashi ya jajjera mata wasu irin shining beads a jikin gashinta masu ɗaukar ido. Ɗage gira yayi Sannan yace "Toya kikaga salon nawa? Fatan yayi Miki? Ɗaga kanta tayi alamun eh" "Okay to abani marki" Nauyi bakinta yayi mata ga matsananciyar kunya data rufeta sam saita kasa buɗe laɓɓan ta tayi magana. "Okay kawai bari a wuce gurin domin na fara lura kema fa kinada buƙatar kasancewa da mijinki kamar Yadda shima yakeda buƙatar kasacewa dake" "Ba haka bane yaya! Wallahi munyi kyau 100%" Wani irin smirking yayi na ganin tsantsar wauta da yarintar Nawaz a fili "Okay to yanzu wace kyauta za'a bani tunda aikina yayi kyau? Nan ma dai shiru ta kumayi batace komai ba, "yanzu dai abar zancen nan tunda naga kina shiga takura, and kuma Ni nafison na ganki cikin walwala" Hannunta ya riƙe ya jata falour zuwa dining area, wasu irin haɗaɗɗun royal lunch sets tagani jere a saman dinning ɗin wanda batasan sanda aka jera su ba. Kujera yaja mata ya zaunar da ita sannan shima yaja guda ɗaya ta gefen ta ya zauna, bubbuɗe abincin yayi tare dayin serving ɗinsu a plate guda ɗaya, cokali ma guda ɗaya yasa, harda drink ɗin daya Zuba a tumbler ɗaya ya zuba. One spoon yayi sannan ya ɗibo wani ya nufi bakinta dashi, babu yanda ta iya haka ta buɗe bakin ta amsa. A haka dai sukayi ta cin abincin tare, harta drinks ɗin Idan yayi sipping saiya sa mata tumbler ɗin a baki itama tayi. Tace ta ƙoshi amma da kyar ya barta, cicciɓarta yayi suka koma kan gado, kwantawa yayi ya ɗora kanshi a saman cinyarta tare da cewa "dubamin ƙwarƙwata" Zaro ido Nawaz tayi "hu'um ƙwarƙwata fa kace? A wannan gyararren gashin naka ne za'a ga ƙwarƙwata? "Eh mana baza'a rasa ba" cewar Aayaan Yana daɗa gyara kwanciyar shi" "Kazanta ce fa take kawo ƙwarƙwata, kuma yanzu duk gyaran kan nan naka saikayi tunanin za'aga ƙwarƙwata?" "To Shikenan duba ki gani Idan bakiga ƙwarƙwata ko ɗaya ba ki zaneni " Gashin kanshi me kama dana ƴan India (koda yake ai shima jinin Pakistan ne) ta fara kamawa tana rabashi sala-sala tana dubawa, sosai gashin ya bata sha'awa musamman fatar kasan gashin, wato fatar kanshi, fara ce sol har wani yellow yellow takeyi domin tafi ko ina a jikinshi fari. Saida tabi duka kan ta duba amma babu abinda ta gani, lura tayi yayi barci sai kawai ta lallaɓa ta sauke kanshi daga cinyarta ta miƙe zuwa bakin dressing mirror, comb ta ɗauka da man gyara gashi sannan ta dawo ta maida kan nashi saman gwuiwarta yanda yake ada. Kwokwonto takeyi Anya barci yakeyi ko kuma yauma likimo yayi mata? "Yaya! Yaya!! Yaya!!! Sau uku a jere ta kira sunanshi, jin be amsa ba yasa ta kama hannunshi ta ɗaga, yararaf ya faɗi Alamun barcin da yakeyi ma yayi nisa. Ƙyalƙyalewa tayi da dariya " Hmmm Nidai Ina ganin ta kaina a garin nan, daga zuwanmu amma nayi ciwon kai yafi sau huɗu, dama haka auren yake ayita kalle maka jiki, nifa kawai don inajin tsoronshi ne amma wallahi da bai isaba, hmm gaskiya yaya Aayaann ƙarshe ne sam baya jin kunyata, yanzu don Allah ji yadda ya saki jiki yana barci bayama tsoron naje na gudu, au to idan na gudu ma wa na sani? sai kuma ta ƙyalƙyale da dariya. Duk abinda take yi yana jinta, so yake ya ƙarar da yarintarta a yau, maganganun data gama sunso su sashi dariya amma ya kanne da ƙyar. Man ta dage ta riƙa shafa mishi akan sannan ta ɗauki comb ɗin idan ta taje saita yi style dashi sai kuma ta ɓata ta kuma yin wani style ɗin, daga ƙarshe dai itama taji barci me nauyi ya kamata, saman ƙirjinshi ta faɗa ba don ta shirya Ba itama ta fara barcin. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Tuni hassu an ware an maida jiki sam babu abinda yake damunta yanzu illa ƙosawa da tayi a cire mata zaren ɗinkin, kuma gashi Lokaci beyiba, abinda yasa yayi saurin haɗe wa ma saboda yawan shiga Ruwan dumi da takeyi ne da kuma abinci mekyau da take ci, ga kula ta musamman da Inna zuwairah take bata .. A jiya da dare ma saida Mummyn Aayaan da Mummyn sarfraz suka saci hanya sukazo suka duba ta, ba ƙaramin daɗi sukajiba ganin yadda ta warware tana sabgoginta. Allah ya taimakesu har suka koma babu wanda ya lura basanan. Kowa ya shirya don yau ake saran duka baƙin zasu koma gidagensu, alokacin kuma Ummin Nawaz taji tana son zuwa gidan inna talatu sannan daganan ta ɗan leƙa umma taga wace waina take toyawa, ko babu komai ai Zaria ta zama gari a gareta, kuma Inna talatu mutum ce Sannan tanaso su ƙarasa Maganar Auren Nawaz da suka fara ta waya. And kuma tasan idan taje gida bazata rasa abinda zata ɗauka ba wanda zaiyi mata amfaniba, tunda dai har zuwa yanzu Abban Nawaz yayi ɓatan dabo, babu shi babu labarin shi. Ammanta ta roƙa akan cewa ko awa ɗaya aɗan bata taje gidan inna talatu, dama a nata idan har Allah yasa an bata to saisu leƙa gidan umman tare da talatu ɗin. Da kyar Amma ta yarda, kasancewar su Uku za'a maida a tasu motar, dayake group group aka raba tafiyar Kasancewar kowa da inda ya nufa. Mummyn Aayaan ce tasa baki akan su ɗaga tasu tafiyar zuwa gobe idan Allah yaso saisu tafi tare da ita, hakan nema yasa Amma ta yarda Ummin Nawaz ɗin ta tafi gidan inna talatu ɗin. Aikam koda ta isa ba ƙaramin girgiza tayiba jin cewa wai Nawaz ta taɓa gudowa gurinta harta ƙaraci zamanta ta koma amma bata saniba. Sosai take mamakin ita kuwa inna talatu wace iriyar Aminiyar ƙwarai ce? Ace ki riƙe ƴa har ki gyarata amma babu wanda yaji! Itakam dame zata iya biyan ta ne?" Bayan sundan sha hirar yaushe gamo ne ummin Nawaz ta roƙi Inna talatilun akan ta taimaka ta rakata gidansu, tanaso taje taga ya dakinta yake. Babu musu inna talatu ta yarda, shiryawa sukayi suka ɗauki hanya...... *ENGLAND..........* A ƙalla saida suka kwashi lafiyayyun awa uku suna barci, koda suka tashi Alwala sukayi Aayaan ya jasu jam'i, suna zaune babu wanda yake cewa ɗan uwanshi ƙala, illa dai Aayaan yakan kalli Nawaz akai akai yayi mata murmushi. Knocking ɗin ƙofar ɗakin akayi, Nawaz ta tashi zata buɗe yace ta koma shi zaije. Babban kwali ya shigo dashi ga uban nauyi, cewa yayi sako ne mummy tace a tawo miki dashi ta jirgin kaya buɗe kiga menene da menene? Koda suka farke gum ɗin babu abinda Nawaz tagani illah kayan magungunan da suka tawo dasu daga sudan, gefe guda kuma aya ce mai uban yawa, wasu abun ma bata gane musu ba, bayan turaruka da humrar da suka tawo dasu daga Sudan Saida taga wasu sababbin da bata sanma dasu ba, ga uwar gumba nan him da dai sauran su, ɗan yatsina fuska tayi ta maida kwalin ta rufe. "Malama ya za'a yi kisani a duhu, fisbilillah kin buɗe abu kin duba kumani kinsan ban san meye ba sannan kin maida kin rufe" "Kayayyaki ne fa kawai" "Ko menene kawai kiyi min bayanin nima zanga ko zai amfani" Zaro ido Nawaz tayi tana neman yanda zata kufcewa wannan Abu da Aayaan yake neman tattago mata. *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *69* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Sosai fa Aayaan ya dage akan shifa saita yi mishi bayani, ita kam Nawaz ko mai zeyi mata bazata iya yi mishi bayanin wannan Abin kunyar ba. Miƙewa tayi tace "bari naje bathroom na dawo" "Okay to muje na raka ki" "No pls kabarshi zani da kaina" "Okay to kiyi sauri kizo kimin bayanin" "To" Nawaz tace tare da yin Hanyar bedroom ɗin, tana tafiya shikuma yajanyo kwalin zuwa gabanshi, bubbuɗewa yakeyi yana cirosu yana ajiyewa a gefe, ko wanne ya ciro saiya karanta jikin kwalinashi ko robarshi, yawanci rubutun da Larabci ne sai English, hakan yasa duka ya fihimci magungunan na Meye! Murmushi yayi yace "WOW WOW WOW! Gaskiya ina ƙaunarki Mummy na, yanzu dama duka wannan Abin duk danni akayi shi, gaskiya dagewa zanyi ta riƙa shansu yadda ya kamata... Hajiya Nawaz kam tana shiga bedroom ɗin ba bayi ta shigaba don dama babu abinda takeji saman gado ta haye abinta taja duvet ta rufe jikinta, aikam bata ɗauki wani lokaci mai tsawo ba barci yayi gaba da ita. Shi kuwa goga Aayaan yana nan ya dage sai ciro kayan yakeyi yana daɗa bin kowane label yana dubawa, waɗanda basuda rubutu a jikinsu kuma sai dai ya kalla ya jujjuya ya ajiye. Saida ya gama fito dasu duka Sannan yaga wata envelope a ƙasan kwalin, aikam beyi wata wata ba ya ɗauketa ya buɗe. *_Assalamu alaikum_* _Daugter ina fatan kun sauka lafiya, Allah ya albarkaci zamanku ya dauwamar da farin ciki mai ɗorewa a tsakaninku_ _Inason don Allah Don darajar Annabi daughter kitaimakeni kirika shan magungunan nan domin zasu taimaka miki matuka, and idanma Akwai wani abun daya shige miki duhu pls ki kira Aseey zatayi miki bayani, so nakeyi ki yakice tsoron nan da kika jibgawa zuciyarki_ _And kuma Ni burina duk sanda zaku dawo ya zamana an tawo mana da tsarabar ƴar England ko ɗan England_ Haka dai Aayaan yabi duka rubutun yana karantawa sinka sinka har zuwa inda mummy tace _A gaida Min da Aayaan ɗin kuma kice nace kullum ya riƙa tunawa da Alƙawarin daya ɗaukar min, na barku Lafiya, Allah ya haɗa kanku_ Murmushi yayi ya maida takardar ya ninke yadda take Sannan ya Maida ta Cikin envelope ɗin ya sakata a cikin kwalin sannan ya Maida kayayyakin ciki. Ganin shiru Nawaz ɗin bata dawo ba yasa shi miƙewa ya nufi bedroom ɗin, murmushi yayi ganinta tana barci lakadan "hmmm sweet heart manya, Allah dai ya barmu tare" Cikin bargon shima ya shiga tare da janyota ƙirjinshi yana rungumeta tsam, "ita batada wuyar barci ne? Naga fa bamu daɗe da tashiba amma harta kuma komawa, ko batajin daɗi ne? Jikinta ya taba ko zaiji tracing ɗin zazzaɓi amma bejiba, girgiza kai kawai yayi ya cigaba da kallon fuskarta. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Kasancewar ummin Nawaz nada sanyi da karayar zuciya tana ganin umma ta fashe da kuka, kuka takeyi bilhaƙƙi tana tambayarta meyafaru har ƙafarta tayi haka? Itama umman kuka ta hau yi tana duba irin zaman cusguna musu data riƙa yi amma ace har yanzu ita bata riƙe ta da wani abu ba, wato har kuka takeyi saboda wani Abu mara kyau ya sameta, nadama da dana sani ne suka ƙara rufeta da tsanar kanta. Itakam ummin Nawaz cewa tayi bazata koma Maiduguri ba tunda umma batada lafiya, zata zauna ta kula da ita har zuwa sanda Allah zai yanke jinyar ta samu lafiya, idan da rabo ma sai Abban Nawaz ya dawo. Inna talatu kam wani ƙululun baƙin ciki ne ya cika mata zuciya, "wai yanzu duk cutarwar da umma tayi musu ita da Nawaz tana nufin ta manta kenan? Gaskiya sanyin zuciyar Rahma yayi yawa...., Tana ganin idan itace ma saidai tace Allah ya sauwaƙe ta ɗauki Abinda zata ɗauka tayi gaba, amma babu yadda za'ayi ta zauna jinyar umma. Kafin wani lokaci ummin Nawaz ta zage ta gyara falourn da umma take zaune, ta fitar da komai tasa omo da hypo da IZAL ta wanke shi tass sannan ta shiga dakinta ta ɗauko katifar Nawaz da zanin gadonta ta sawa umma sannan suka ciccibeta a hankali suka ɗora ta akai, harta poo ɗin da umma take bayan gida a ciki Saida ummin Nawaz tayi mishi wanki na musamman Sannan ta kwashi sauran Kayan data cire a shinfidar umma ta da ta wanke su tass. Inna talatu ce duk take tayata amma cike da mamakin irin sanyin halinta da rashin riƙon ta. Ba Ita ta samu ta huta ba sai da yamma tayi liss, wayarta ta ciro ta kira layin Amma take sanar da ita halin data je ta tarar da Umma, itama Amma ɗin bataji daɗi ba, sosai ta nuna alhininta Sannan tayi mata addu'oi da fatan samun lafiya, bata ce dole saita bisu sun koma Maidugurin tare ba saboda ai ciwon abokiyar zamanka kamar naka ne, tunda kaima wata Rana zaka iya yin ciwon kuma itace zata taimaka maka. Bayan sun gama wayar ne Amma take shaidawa Mummyn SARFRAZ da Mummyn Aayaan Abinda ya faru. Mummyn SARFRAZ daɗi ne ya rufeta sosai, har ji takeyi kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha saboda farin ciki, take ta tuna labarin da Nawaz ta bata na irin cutarwar da Umma tayi musu, daga ƙarshe ma duk cutarwar bata yi mata ba saida ta sa yan shaye-shaye suyi mata fyaɗe, dabadon Allah ya kare taba da yanzu ba'a san a Wane hali takeba. Sosai Mummyn Aayaan taketa jimami, wayarta ta ɗauka don kiran Aayaan ta sanar dasu, aikam babu shiri Mummyn SARFRAZ ta hanata "kada ki kira yara suna can suna farin ciki ki tada musu da hankali akan wata muguwa chan" Buɗe baki Mummyn Aayaan tayi tana mamakin kalaman Mummyn SARFRAZ, "tabbas nasan zakiyi mamakin maganganun dana faɗa, amma zaki dena mamakin muddin na feɗe Miki biri har wutsiya" Tsaff Mummyn SARFRAZ ta kwashe komai data sani game da umma ta faɗawa Mummyn Aayaan, "girgiza kai kawai Mummyn Aayaan takeyi don tama kasa magana, jin Abin takeyi kamar almara, "lailai Akwai mugaye a duniya" abinda ta iya faɗa kenan. "Don Allah gobe da safe mu shirya muje inaso inga idon mara imanin" "To kada ki damu In'sha Allah da sassafe zamu shirya muje tare dasu Amma kafin su tafi" Cewar Mummyn SARFRAZ Achan gidan su Ummin Nawaz kuwa sam bata lura da halin da jamila take cikiba saida ta natsa ta ɗan huta tukuna taga Jamila da ciki riƙi-riƙi... "Jamila aure tayi bayan mun tafi? Sai kuma tayi shiru data tuna duka dududu watansu nawa da tafiya da har Jamila zatayi ƙaton ciki haka? Umma na sharar ƙwalla tace "yaran yanzu ne ka haifesu baka haifi halinsu ba, yarinyar nan a makaranta fauziyyah taje ta tawo da ita da wannan ƙaton cikin... Salati Ummin Nawaz ta Fara tana sallallami, gaba ɗaya ta ruɗe kai kace Nawaz ce ɗauke da cikin "Yanzu Jamila kinyiwa kanki damu iyayenki da ƴaƴanki gata kenan? Bayan dokar Allah da kika keta kin jefa kanki a rayuwar wahala da ƙunci ga tarin zunubai da kika jibgawa kanki, to yanzu yakike so ayi, me kikeso muce wa shi Abinda zaki haifa, bayan haka ma shi meye makomarshi a idon duniya?? Fashewa da kuka Jamila tayi tana girgiza kai tare da cewa "nashiga uku, wayyo Allah na, Allah kasa in mutu lokacin dazan haihu" Toshe mata baki ummin Nawaz tayi tare da cewa " bakida hankali ne Jamila! Meye kike kirawa kanki mutuwa? Ba gara ki rayu ba kiyita neman Allah ya yafe miki ba" Umma ma kuka takeyi kashirɓan tana danasanin lalata rayuwarta da tayi, tunda take da ummin Nawaz bazata iya nuna Abu guda ɗaya tace tayi mata shiba, amma duk da haka kishi ya rufe mata ido ta riƙa Neman Yadda zata halaka ta da ƴar ta. Garin haka kuma ga lalurar data janyo wa kanta.... Sun daɗe Anan zaune ummin Nawaz tace bari taje ɗaki itama ta gyara ɗan abubuwan da ba'a rasa ba, amma idan ana buƙatar wani abu ko kuma umman zata hau poo a kirata. Dama Inna talatu a ƙage take, suna shiga ɗakin ta fara masifa "gaskiya Rahma bakida zuciya a cikin kirjinki, yanzu fisbilillah duk cin zarafi da cin mutuncin da matar nan tayi miki shine zaki zage kina bauta mata haka? Yanda nayi imani da Allah haka nayi imani cewa dakece hakan ya faru dake dariya zatayi, ƙilama saita zuba ruwa a ƙasa tasha saboda farin ciki. "Haba ƙawata, aini duk abinda kikaga ina yi mata to inayine saboda Allah da kuma saboda mijina Muhammad, kuma ai zaman tare ya wuce komai, naga koda a gidan haya muka haɗu zan iya yi mata ma Abinda yafi haka balle kuma Wadda muka haɗa miji" "Lallai Rahma! Wallahi zuciyarki mai kyau ce, Allah ya ƙara miki haƙuri da kyawawan ɗabi'u" Murmushi ummin Nawaz tayi tare da cewa "Ameen" sannan ta maida kanta taci gaba da kakkaɓe ƙurar da take kakkaɓewa. "Kafin isha'i nakeso na tafi gida" cewar inna talatu "To bari muyi Sallah saina rakaki, ai wallahi kimmayi ƙoƙari sosai, Nagode Allah ya bar ƙauna da zumunci " "Ameen" Cewar inna talatu itama ta miƙe tana gyara wasu abubuwan *England........* Koda suka tashi daga barci dare ya riga da yayi sosai, Aayaan ne yace ya kamata su ƙara yin wanka saboda yanaso suje wani store dayayi mata oder ɗin kaya ta online tun suna Nigeria ..... Fir Nawaz tace itafa atafalfal bazata ƙara yin wanka ba, kuma a zancen gaskiya tanaso tayi wankan kawai dai bataso yace zaiyi mata ne.. Tsaff ya gane me take nufi shiyasa shi kuma ya dage akan dole fa sai anyi wankan nan ko kuma ido ya raina fata. Dataga abin da gaske ne sai kawai tace to ta yarda don alamun su fara nuna mata zata jawa kanta idan bata haƙura da iya wankan ba to zata iya jangwalo me gaba ɗaya. Tanaji tana gani yanzuma Aayaan ya dage yana mata wanka, rabi taɓe-taɓe rabi shiririta quarter ne wankan, yauma dai kamar kullum Idonta a rufe yake gam. Tana cikin jacuzzi ɗin shima yayi nashi wankan sannan ya nannadota ya fito daga bathroom ɗin, haka ma yanzu duk shi ya shafa mata mai yasa mata undies, duk dai abinda ya kamata haka ya gama yi mata amma koda wasa ta ƙi yarda ta buɗe idonta. Shikam ko a jikinshi domin nishaɗinshi ma yakeyi. Yanzu ma yayi yayi ta buɗe idon taƙi, yayi dabarar namma taƙi, ganin bafa zata buɗe ba. Yasa ya ciccibeta ya ɗora saman gado tare da zuge zip ɗin rigar daya sa mata yana ƙoƙarin cire mata bra. Babu shiri ta buɗe ido tare dacewa "nifa da barci ne ya fara ɗaukata shiyasa banji sanda kake cewa in buɗe ido ba" "Kin rigada kin makara, domin na kai bango, bazan iya hakuri ba a halin yanzu, i am sorry" Kuyi hakuri da wannan 🙏🙏 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *70* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Fashewa tayi da kuka tare da cewa "Nidai gaskiya na gaji da garin nan ka maidani gida" Tashi zaune Aayaan yayi tare da maida mata ZIP ɗin ya rufe "meyasa ba kya son garin nan?" "Kullum mutum yana daki babu motsin kowa, and kuma Koda na fita ba irin mutanen dana saba gani zan gani ba" Murmushi yayi "To yanzu dai Nasan daga zuwanmu ba kadaici zallah kikewa wannan ƙorafin ba, tunda har yaushe mukazo da zakice kullum, kawai dai a takaice kice kinaso ki riƙa ganin ƴan Nigeria" Ɗaga kanta tayi alamar "eh" "Okay to Yanzu abinda nakeso dake shine ki tashi mutafi store ɗin kinga daga chan ma sai mu tawo da sabuwar laptop Wadda zanyi miki registration a online, gobe saiki fara zuwa" Zaro ido Nawaz tayi "ina zan fara zuwa?" "Wata makaranta ce ana ce mata *LIFE SCHOOL* mutane ne kala kala acikin Makarantar, kamar ke Yanzu da kike complain nasan idan kika fara zuwa Makarantar zakiji daɗin ta sosai saboda suna koya yadda zaka zauna da ko wane irin jinsi da yaren ɗan adam, kuma suna koya yadda zaka zama freely ako wace irin ƙasa ka tsinci kanka, ba iya nan ba suna koya kalar dressing ɗin ƙasashen duniya da girke girkensu. "Hope u're interested?" Murmushi ne ya kufce mata "yea naji daɗi sosai sosai, thanks alot" Gira ya ɗage sama "kiss nakeso a madadin godiyar" "Ni dai Allah zan fasa fitar" "I'm sorry to, yanzu ɗauko veil a cikin closet ɗin chan mutafi" "Yaya wai a ina ka samu kayan mata ne? Dazu kasamun wata riga, yanzu ma kasamun wata kuma kace naje na ɗauko veil yanzu. Gyararriyar ƙasumbarsa ya shafa da hannunshi na hagu sannan yace "yea! Tun kafin mu tawo nasa aka min order ɗinsu a reception sannan aka kawo min su ɗaki aka shirya" "Kenan wannan ɗakin kane😳😳? "Yea permanent ɗaki nane duk sanda na sauka a nan ƙasar, gwamnatin Britain ce ta bani shi har sai sanda nayi retire tukuna, idan ma Anan ƙasar na dawo da zama to har saina mutu" Jinjina kai Kawai Nawaz takeyi tana mamakin Matsayin da akaba Aayaan kuma ba'a cikin ƙasar Shiba. "Sweetheart muje kada time ya gudun mana, idan muka dawo saiki tambayeni duk Abinda kikeso zan baki amsa In'sha Allah" Da kanshi ya miƙe ya buɗe closet ɗin ya dauko mata Babban mayafi wanda yake haɗe da ƙaramin hijab, sa mata yayi ya gyara mata Yadda ya kamata sannan ya kama hannunta yace "muje sweetheart" Binshi ta fara yi ahankali saboda takalmin daya sa mata me uban tsini, hakan da takeyi sai yayi kamar tana yanga ne, card ɗin daya buɗe ƙofar dashi ɗazu sanda suka zo ya kuma sawa a sensor ɗin jikin ƙofar, ai kuwa ƙofar ta rufe ruff kamar ba yanzu suka fito daga cikin taba, button ɗin lifter ya danna ƙofar ta buɗe suka shiga ciki. Cikin ƴan mintoci suka sauka ƙasa, gani tayi kawai Aayaan ya buɗe wata shu'umar mota ya saka ta a ciki Sannan shima ya shiga. Mamaki Kusan kasheta yayi, tasan dai tare suka sauka ƙasar nan kuma tunda suka shiga ɗakin be fito ba suna Tare to yaushe ne har ya siya mota kuma? Gira ɗaya Aayaan ya ɗage mata "Are you surprised? Don't be! Saboda har indigene ɗin ƙasar nan inada shi, kinga kuwa this is nothing Koh? Ƙifƙifta ido kawai Nawaz tayi tana kallonshi a sace... Smirking yayi yaci gaba da tuƙi da hannu ɗaya while ɗaya hannun ya riƙe hannun Nawaz yana matsa mata tafin a hankali. Ƴar taƙaitacciyar tafiya sukayi suka isa wani classic and unique boutique, tundaga waje yake ƙyalli, harta ƙofar shiga cikin boutique ɗin designer ce, Komai nagurin me ajih ne. Ɗaukar ta yayi in a bridal way suka shiga ciki, tunda suka shiga ma'aikatan wajen ke gaishesu. Guri me kyau aka tanadar musu sannan aka Kawo musu ruwan roba Tare Da tambayarsu ko suna buƙatar wani abun. Ɗaga musu hannu Aayaan yayi Alamun basa buƙatar komai, "where is Affiah Aliyuo" Aayaan ya tambayi ɗaya daga cikin staff ɗin wajen. Ai kuwa da sauri tabi wata hanya tana ƙwalawa Affiah kira. Cikin ƴan daƙiƙu Affiah ta karaso tana murmushi tare da gaishe da Aayaan ɗin cikin sanayyah, Sannan ta gaishe da Nawaz itama cikin girmamawa daga bisani kuma ta buɗe wata kofa ta shiga ciki, fitowa tayi janye da wasu akwatuna manya guda biyu Sannan wasu yan mata suma guda biyu suna janye da guda bibbiyu suma, That means guda shida kenan "Sir ga kayan da aka haɗa mata, yanzu abinda za'ayi kafin ta tafi ta duba taga Idan Akwai abinda beyi Mata ba sai a chanza mata" "Nop i trust you Affiah, idan ma akwai wanda beyiba zansa a dawo dasu, duk da harshen Nasara suke wannan zancen. Ɗibar akwatinan wasu ƙatti majiya ƙarfi sukayi tare da kaiwa cikin motar da su Aayaann suka zo da ita, tashi suma su Aayaan din suka yi suka fita, saida ya saka ta acikin motar ya rufe Sannan ya koma ya shiga ɗaya gefen don yin driving. Ita dai Nawaz ta zama mutum mutumi, mamakin wannan lamari takeyi "wai ita wa ta aura ne?" Cikin wani super store suka shiga wanda ya haɗa Komai na kayan rayuwar duniya, bayan su abinci ga kayan sarrafa abincin nan su kayan makaranta irinsu littattafai dadai sauran abubuwan buƙata. Gefen laptop sukaje Yace ta zaɓi wadda takeso, kasa zaba tayi saboda kunya, wata Apple ya zaɓar mata golden colour me ɗan banzan kyau ita Kanta saida taji cewa tayi Sa'a matuƙa "kinga wannan tayi Miki? "Cikin zumuɗi Nawaz tace "tayi min sosai sosai" "Are you sure? Taki ce fa wannan, Ni tawa tana gida, don haka ki zaɓi Wadda tayi miki bakida Matsala" "Allah tayi min sosai, thank you very much, may Almighty Allah bless you and All your family, especially mummy" Wani irin daɗi ne ya rufe Aayaan, yana matuƙar jin daɗin irin addu'oin da Nawaz take yi mishi, Gashi ita bata raina abu komai ƙanƙantarshi. Daɗin dayaji yasa ya riƙa jidar mata abubuwa kama daga jaka, takalmi, mini hijabs, veils, turaruka, mayukan sa taushi da santsin jiki irin na turawa sarƙa da Bangles masu kyau kamar wanda zai buɗe wani madaidaicin boutique. Haka ya gama haɗa kayan duka Sannan ya basu Master card dinshi sukayi debiting ɗin kuɗin siyayyar suka kai musu mota. Yanzun ma dai ciccibarta yayi ya sata a motar shima ya shiga suka ɗauki hanyar komawa gida. Yana lura da Nawaz sosai, tunda suka fito take hamma, yanzu haka idonta har kadawa yayi Alamun barcin takeso tayi hani'an Shiyasa ya ɗan ƙara speed ɗin motar kada ta chutu da yawa, har sun kusa isa gida ya tuna cewa yaga wani text da mummy ta turo mishi na cewa ya siya wa Nawaz fresh milk da yawa a zuba a fridge saboda dasu zata riƙa shan magungunan ta, Sannan kuma ya nemar mata injin yin kunun Aya saboda shima zata riƙa yi... And ta kara da cewa ya tabbatar tana cin Kayan itatuwa sosai musamman dangin su Apple, kankana, gwanda, inibi da ayaba, kuma ya riƙa siyo mata gasashshiyar kaza kullum. Reverse yayi ya koma wani store dake kusa dasu, Carton uku na fresh milk ya siya sai fresh chicken pack biyu Wadda da safe zasuyi Amfani da ita, anan bakin gurin yasa akayi mishi packaging ɗin fruits iri iri Saboda umarni Mummy.. A wahale Nawaz ta isa gida domin wani wahalallan barci ne yake cinta a Ido, kamar zata faɗi haka ta riƙa ji, Gashi kuma Aayaan ya tada fitina akan saiya yi mata wanka kafin su kwanta, ita dai ta rasa wannan jafa'i, wanka wanka wanka kamar kwaɗi, banza tayi dashi don ta fara gajiya, tanaji ya ciccibeta ya cire mata kaya Sannan ya zunduma ta a cikin jacuzzi, haka ya gama kiɗanshi ya gama rawar shi bata ko buɗe ido ba balle ta tanka mishi. Tanaji yasa mata kayan barci ya feshe ta da turare ya ɗora ta a ƙirjinshi yaja musu duvet, kusan ince daga ɗaya Nawaz Neman barcin tayi ta rasa domin Aayaan ya isheta da taɓe taɓe, daga ya taɓa chan saiya ja chan, ya tsotsi chan ya matsa chan har sauke numfashi yake yi da sauri da sauri, ganin yadda ya matsa da yawa yasa tsoro ya kama Nawaz,. Aikuwa take jikinta ya fara rawa, shi kuwa Aayaann jin jikin Nawaz ɗin yana rawa ya gane Cewa ta tashi. "Sweetheart kin tashi?" Shiru tayi tana tsoron kada tace eh ya zarce Murmushi Aayaan yayi "wai duk tsoron ne haka?, To ki saki jikinki babu abinda zan yi Miki, kin manta na Miki alkawarin sai kinaso? And I always keep my words. Bata tanka mishi ba saidai jikinta ya dena rawar, a haka dai tana jinshi har barci ya kuma kwasheta. Yauma koda suka tashi da asuba shi yayi mata wanka ya shirya ta sukayi Sallah sannan suka koma barci, sai wajejen ƙarfe tara suka farka, kamar jiya haka yauma taga abinci kala kala jere a dinning batasan wa ya jera ba, bayan sun gama break fast ɗin ne Aayaan ya dauko sabuwar laptop ɗin daya siya mata jiya ya saita mata Komai tare dayi mata subscription na shekara ɗaya. Bayan ya gama haɗa komai na laptop din yace ta shirya suje Makarantar Kawai yayi mata registration ido na ganin ido tunda jiya Allah beyi za'ayi ba, "to ai a shirye nake" Hararar wasa ya balla mata tare da cewa "Nifa bana zama da ƙazami" Zumbura baki tayi " to Amma yanzu dai don Allah ka bari nayi wankan da kaina tunda kaga sauri mukeyi " "To kije kiyi, amma Ni zan shirya ki" Batare da tace komai ba ta juya ta shige bathroom ɗin. Kafin ta fito ya buɗe ɗaya daga cikin akwatinan da suka amso jiya ya zaɓo mata wasu irin designers ɗin riga da wando ƴan Turkiyya, rigar sakakkiya ce Sannan tsayin ta har gwuiwa sai wandon shima dogo me faɗi. Babban veil ya ciro mata me ruwan madara Irin me haɗe da hula da mini hijab ɗin nan, dayake kayan peach colour ne. A Saman gado ya ɗora su sannan ya miƙe ya fita falour don ya haɗa Mata magungunan ta, yanaso ta fara sha daga yau har zuwa Lokacin daya ɗibarwa kanshi... Kofuna guda Uku Ya ɗauko tare da robar madara guda biyu sai magungunan kala kala, harda gumba da Tsumi.... Mamaki Abin ya bashi sanda ya dawo ganin daga fitarshi wai harta fito daga wankan ta shirya, murmushi yayi "Anya ba sai kin koma an chanza wankan nan ba? Naga kamar ojoro kika yimin" Dariya tayi "Allah yaya na fita" "Ooh Nidai nace a taimaka adena ce min yayan nan asa min wani suna na daban amma anƙi" "Zansa maka In'sha Allah Kawai dai ban gama tunanin wanne ne ya dace dakai bane" Murmushi yayi "shikenan to pls idan an tashi zaɓowa a zaɓo min me daɗi" Rufe fuska tayi alamun jin kunya, kusa da ita ya matsa ya mika mata magungunan tare da cewa "kiyi sauri kisha saimu tafi" Babu musu ta amsa, tasha da yawa saboda basuda ɗaci kuma barin ga madara, Goge mata baki yayi da tissue sannan ya Gyara mata mayafin ya fesa mata turare ɗan daidai sannan ya zaɓo mata wata Yar ƙaramar jaka me kyau wadda zata shiga da kayan haɗe da takalminta. Tsaff suka fito gwanin sha'awa, tsaff tsaff dasu kamar ka sace ka gudu.... Sanda suka isa makaratar Saida ya tabbatar Komai Saida ya biya kuɗinshi har zuwa sanda zata dena zuwa Makarantar, har aji ya kaita Sannan ya juya ya tafi da alƙawarin zai dawo ƙarfe huɗu ya ɗauke ta, dayake ƙarfe biyu ake shiga ajin a tashi huɗu. Nawaz taga ikon Allah, mutane kala-kala iri-iri haka ta gansu, iya kallonka dole kaci karo da halittar da baka taɓa cin karo da irin taba.... Dayake karatun ana yi musu na awa ɗaya da rabi ne to sauran minti talatin ɗin sai a barku Ku tattauna da sauran ƴan ajin yadda zaku saba dasu sosai. Malamin na fita wata mata ɗauke da jinjiri wanda a ƙalla bazai wuce wata Uku ba ta ƙaraso kusa da Nawaz ta zauna "ƴar uwa wallahi tunda mijinki ya shigo dake nake Allah Allah malamin nan ya fita saboda inyi hausa inɗan ji daɗi, tunda mukazo ƙasar nan bana ko wane yare sai turanci" Murmushi Nawaz tayi mata tare da amsar yaron "to mijinki fa? Ko baya kusane?" "Hmmm ai dogon labari ne, bayajin hausa sam" "Allah sarki! To yaudai Allah ya haɗa mu" "Wallahi kuwa, Allah dai yasa zaku daɗe a ƙasar " cewar matar tana kallon Nawaz cikin jin daɗin haɗuwa da ita. "Eh inaga zamu jima In'sha Allah" "Masha Allah naji daɗi sosai, To Nidai sunana Zainab Ibrahim s lame, Ni Yar jahar kano ce a Nigeria, wannan ɗan naki kuma sunanshi sudeis, mijina kuma ɗan Sudan ne, mun haɗu dashine a jahar Jigawa sanda naje ganin kakannina" "Allah sarki, gaskiya naji daɗin haɗuwa dake maman sudeis, Allah ya ɗorar da ƙawancenmu" ɗaga sudeis ɗin Nawaz tayi tana mishi wasa shi kuma sai ɓangala dariya yakeyi. "Iyye ashe Sheikh sudeis baka ƙyuya" cewar Nawaz tana daɗa ɗagashi sama. "Aikam dai bai fara ƙyuya ba tukuna, har roƙon Allah nakeyi akan Allah yasa kada yayi ƙyuya wallahi" "Allah yasa kada yayi" "Ameen" Cewar maman sudeis Gyaran murya Nawaz tayi Sannan tace "Ni sunana Madinatul munawwarah Muhammad, amma anfi cemin *Nawaz* Ni yar Zariya ce, amma iyayena Yan Maiduguri ne, shima mijina da surukaina duka yan Maiduguri ne, achan Maidugurin ma muka haɗu, and kuma bamu daɗe sosai dayin aure ba. "Masha Allah Madinah, gaskiya naji daɗin haɗuwa dake, ashe Amarya ce! "Sunne kai Nawaz tayi Alamun jin kunya. Miƙewa sukayi Nawaz na rumgume da sudeis suka fita daga cikin hall ɗin zuwa harabar Makarantar suna ɗan tattakawa, maman sudeis tana ta dan nuna mata gurare. Wata ce ta zundumo da gudu itama daga ganinta kaga bahaushiya duba da riga da skirt ɗin atamfar dake jikinta, tana karasowa gurin ta rungumesu "ashe Akwai Hausawa a makarantar nan, wallahi jiya na fara zuwa ga ajinmu chan, babu bahaushe ko ɗaya, na rasa Yadda zanyi. "Ayyah dayake jiya banzo ba" cewar Maman sudeis Nan dai itama ta gabatar musu da kanta, tace sunanta Fatima itama ƴar Zariya ce cikin Tudunwada *Magume* itama bata ɗade dayin aureba suka tawo nan England tare da mijinta. Cikin ƴan ƙalilan ɗin mintocin da suka rage a tashi, sosai Nawaz da maman sudeis da Fatima suka saba da juna sosai, kamar sunfi shekara da sanin juna. Duk sun faɗa mata address ɗin su amma dayake ita bawai tasaba da garin bane bata san inda suke nufi ba. Lokaci na cika saiga motar Aayaan ta sawo kai ta shigo cikin harabar Makarantar, daɗi sosai Aayaann yaji ganin Nawaz riƙe da jinjiri ta sake cikin wasu mata guda biyu da be sansu ba suna hira harda dariya. Kusa dasu ya karaso suka gaisa Sannan yacewa Nawaz "To Madam time yayi fa, idan kuma baku gama hirar ba sai in ƙara miki koda 30mins ne. Da sauri Fatima tace "A'a gaskiya baza'a yi haka ba, ai muma gida zamu tafi, kawai ku tafi. Aayaan ne yace "za'a zo a ɗauke kune ko da kanku zaku tafi? "Da kanmu zamu tafi" cewar Maman sudeis "A wace unguwa kuke? Aayaan yace yana miƙa hannu yana amsar sudeis a hannun Nawaz Faɗa mishi sukayi, ashema duk suna kusa da juna, sai an wuce gidajensu ma tukuna zasu ƙarasa hotel ɗin da suka sauka. Cewa yayi su shiga motar kawai duka ya rage musu hanya, Aikuwa cikin jin daɗi suka shiga suna mishi godiya. Nawaz tace ya bata sudeis saboda yaji daɗin tuƙin amma fir Aayaan yace tabar mishi shi, sai wasa yakeyi mishi, hakan yasa tuƙin nasu a hankali akeyi. Koda aka karaso Kofar Gidan Fatima sai ta sauka tana ce musu sai sun haɗu gobe a makaranta. Tafiya kaɗan aka yi aka ƙaraso gidansu Maman sudeis itama, dakyar Aayaan ya bata sudeis suka shiga gida. Ko a hanya ma sai hirarshi yake ta yiwa Nawaz ɗin, sosai Nawaz tai mamakin yadda farat ɗaya sudeis ya shiga zuciyar Aayaann. Abin Allah sati daya da haɗuwarsu amma wata iriyar shakuwa ta shiga tsakaninsu, har Allah Allah Nawaz takeyi gari ya waye ta tafi makaranta don su haɗu da juna, Maman sudeis Akwai mutunci sosai ga bayar da shawarwari masu amfani, itama fatima akwai saurin sabo, ga mutunci itama kuma akwai yawan ɗebe kewa don tanada faran faran ga wasa da dariya. Tunda suka haɗu Aayaan shike maidasu gida, kuma kullum sudeis yana hannunshi, haka duk sanda Nawaz zata tawo saiya bada su chocolate da abubuwan wasa wai a kawowa sudeis, duk da Nawaz na cewa be iya cin abinci ba amma saiya bayar kullum, fatima ma da maman sudeis ɗin suma Duk ya sai musu wasu dogayen rigunan masu kyau. Aayaan yana mutunta duk wanda yakeson Nawaz shiyasa cikin Lokaci ƙalilan suma su fatima suke mamakin wace iriyar ƙauna Aayaan yake yiwa Nawaz. Yau dama su maman sudeis da Fatima suka yi zasuje gidan Nawaz idan an tashi daga makaranta, Koda aka tashi Aayaan ne ya kwashesu ya kaisu shi kuma ya ɗauki sudeis suka yi waje, sosai ɗakin Nawaz ya burgeshi sai santi sukeyi. Sunsha hira sosai inda sai wajen ƙarfe shida sukace zasu tafi, anan ne fa Nawaz ta rasa me zata basu, tunawa tayi da magungunan ta, samun polythene bag tayi ta zuba musu da yawa, godiya sosai sukayi mata har Maman sudeis tana tsokanar Nawaz da cewa "Ashe Yau kince mai gida ya ɗan ji chanji kenan" ita dai kunya na hana Nawaz yin magana. Rakasu gurin Aayaan tayi suka amshi sudeis don tafiya gida. Cab Aayaan ya Samar musu suka yi sallama suka shiga sukayi hanyar gida, inda shikuma ya ciccibi Nawaz suka koma ɗaki. Cikin yan kwanakin wata irin shakuwa ce mai ƙarfi ta shiga tsakanin Aayaan da Nawaz, ga wani irin body contact Daya kamasu, ɗaya baya zama kusa da ɗaya face saiya taɓa jikin daya. Haka zasuyi ta rige rige wajen ayyuka, har dambe sukeyi wajen cin abinci. Yau ta kama asabar, Aayaan yana zaune yana gyarawa Nawaz ƙumba (Akaifa) bayan ta gama gyara mishi nashi. Knocking ɗin kofar su aka farayi a hankali, da sauri Aayaan ya mike tare da buɗe ƙofar, maman sudeis da Fatima ya gani tsaye suna murmushi, duk sai suka daburce ganin Aayaan sanye da kayan shan iska. Guri ya basu suka shiga ciki inda shi kuma ya ɗauko jallabiya yasa ya bar musu daƙin. Yana fita fatima tace "Madinah bakiyi mamakin dawowar mu yauba bayan shekaranjiya mukazo" " Haba mamaki? Ni farin ciki nakeyi wallahi" "Nifa zuwa nayi idan akwai sauran maganin Nan da kika bamu ki ƙara sam mini" cewar Maman sudeis tana ɗora sudeis akan kujera. "Wallahi Nima haka" Cewar Fatima. "Dariya Nawaz tayi, akwaiku da abin ban dariya Allah" " Hmm wane abin dariya, jiya fa ogana har Cewa yayi zamu koma Umrah, ita kuwa maman sudeis Kinga sabuwar wayar da babban sudeis ya canza mata a jiya da safe" Cewar Fatima cikin muryar da take nuna gaskiya take faɗa daga cikin zuciyarta. Ita kuwa maman sudeis cewa tayi"ashe ba banza ba, dole oganki ya riƙa zargadila akanki yasan abinda yake kwasa" "Nifa amaryace har yanzu" cewar Nawaz tana sunne kai. "Au wani yace kin tsufa? Maman sudeis tace tana ɗaukar Ruwan dake saman table. "Look nifa ba haka nake nufi ba, Ni babu abinda ya taɓa shiga tsakaninmu da ogana, soyayyar da yake min daga Allah ce, amma ba don wani abu bane" Nawaz ta faɗa freely Saida maman sudeis ta ƙware da Ruwan da take sha Sannan ta miƙe da sauri. Kusan a Tare sukace "kai Madinah, don Allah bada gaske kike ba Koh? Miƙewa Nawaz tayi tabi Hanyar dining don Kawo musu abin tabawa, Sannan tace "Allah da gaske" "To mijin nakine beda lafiya ko kuma ke kikee hanashi?" "Hakanan, kalau yake" Tana shiga kitchen Fatima ta Kalli Maman sudeis tace mata ya kamata muyi wani abu fa, inba hakaba Madinah zata kashe ɗan mutane, ace wannan lafiyayen mutumin fanko yake zaune? Nawaz na dawowa tagansu tsaye, cewa tayi " ku zauna mana" "Bazamu zauna ba, kuma daga Yau kada ki sake ki kuma nuna kin sanmu, Ashe dama bakida hankali, ashe muma jahilai ne muna tare da ƴar jahannama bamu sani ba. "To daga yau sai yau babu mu babu ke" Zaro Ido Nawaz tayi tana mamakin ita kuwa metayi haka da zafi? *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *71* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Ummul Kulsum Muhammad ko ince *Nuwairah* ko kuma *chu-chu* duk Wanda dai kika zaɓa Acikin sunayen yayi, Wannan shafin nakine *100%* amma idan zaki dara ayi kaɗan kada ayi ciwon ciki. Sosai idon Nawaz yayo waje domin maganganun su sun ratsa ta, "Yanzu fa muke magana! To me nayi da zafi da har zasuce min Yar jahannama? Ko dai wani Abu mara kyau suka gani a cikin Ɗakin?" Kama hannun Fatima tayi "don Allah sis ki faɗa min me nayi? Ko wani abu kuka gani?" "Lallai Madinah! Ashe bakida imani kuma baki tsoron Allah, gaskiya da Nasan haka kike ko da wasa bazan taɓa zuwa kusa dake ba balle har mu ƙulla ƙawance ba, irin kune kuke jawa waɗanda basuji ba basu gani ba wahala, fushin da Allah yake yi daku ya shafi sauran bayin Allah" Cewar maman sudeis tana ƙoƙarin maida sudeis ta goya. Riƙe sudeis ɗin Nawaz tayi da ƙarfi tare da cewa "Don Allah Don darajar ma'aiki ku taimaka ku faɗa min Abinda nayi Kafin ku tafi, Wallahi zan gyara har dai wanda za'a iya gyarawa ne. Fatima ce tace "kinyi Alkawari?" "Wallahi nayi! Amma Don Allah ku koma ku zauna" "Kaini bedroom ɗin da kuke kwana" Abinda maman sudeis tace kenan ta maida bakinta ta tsuke Jikin Nawaz har rawa yake yi tsabar sauri tayi hanyar bedroom ɗinsu tare da cewa "kuzo muje" Suna shiga babu a inda Maman sudeis ta tsaya sai gaban drawer, buɗe drowoyin tafara yi tana duba cikinsu Alamun tana neman wani abu. Wasu robobine kusan guda Biyar iri ɗaya ta cirosu a cikin drawer karshe, kallon jikinsu tayi sosai tana Nazarin rubutun dake jiki. "Uuhhmmm aini na sani, dole ba haka kawai ba! Wallahi Nawaz Kiyi saurin tuba zuwa ga Allah inba haka ba kuwa kinshiga Uku, ke wallahi idan kika mutu a yanzu ma hmmmm. Ita dai Nawaz dama a tsure take, ganin kuma maman sudeis ta ciro robobin nan tana wasu maganganu saita ƙara tsurewa. Ita dai tasan wadannan robobin na magungunan Aayaan ne da yake sha kullum, bazata manta sanda ta rakashi ya taɓa siyowaba lokacin da yazo gidan inna ya sameta sanda ta gudu Zariya, kullum yanashan biyu da safe biyu da yammah amma dai ita batasan maganin me yake yiba. "Kinga waɗannan robobin? Kuma kinsan wane magani ne acikinsu?" Girgiza kai Nawaz tayi Alamun bata saniba. "To ƙwayoyin kashe sha'awa ne! Mijinki yana sonki kuma yana ƙaunarki, babu Abinda ya rage ki dashi amma ki rasa dame zaki biyashi sai da Wannan Madinah?, Kinsan kuwa irin halin dayake shiga na Rashin samun haɗin kanki? Ni nasan dolece tasa ya nemi maganinnan bawai don son raibane" Fatima ce itama taci gaba da Magana "gaskiya Madinah kin bani mamaki, Ashe wayonki na Banza ne, kinata mutuntamu Ashe mijinki da baƙin cikinki yake kwana yake tashi, kekam da kinsan irin zunuban dake kanki nasan ke kanki ƙyamar kanki zaki riƙa yi, amma it's not late, zaki iya tuba kuma ki gyara. Duk jikin Nawaz yayi sanyi ƙalau, damuwa ta rufeta, tabbas tasan Aayaan yana tausayinta sosai shiyasa ya kyaleta har zuwa yanzu beyi mata komai ba' amma ita batasan yana chutuwa haka da yawa ba da har zai Nemi ya halakar da kanshi saboda ita ba" "Don Allah Maman sudeis da Fatima kuyi haƙuri, Wallahi zan gyara kuma In'sha Allah harshi saina nemi daya yafemin, amma Idan kukace babu ku babu ni ya kukeso nayi a ƙasar nan? Don Allah kuyi haƙuri" "Munji amma gaskiya mu muna nan akan bakar mu har sai munga chanji tukuna, idan bamuga chanji ba to kada ma ki tunkaro mu don bazamu riƙa kula wadda Allah ke fushi da itaba. " Yanzu dai ɗebo mana maganin mutafi tunda dai mu munsan daraja da martabar mijinmu" cewar Maman sudeis tana daɗa yin miri-miri da ido. Simi-simi Nawaz ta fita zuwa store inda Aayaan ya ajiye mata kwalin magungunan, babban mazubi ta samu ta zuba musu da yawa sosai, duk sunsata a vibration tama rasa meke mata daɗi. A chan ɗakin kuma Nawaz na fita Fatima ta tuntsire da dariya "kai Gaskiya Maman sudeis bakida dama, ji yadda kika hargitsa ƴar mutane!" "Haba Fatima ai gyara nayi, kuma naga ke kika bani himma ma akan yin gyaran, ya za'ayi mutum yana mata wahala kamar bawa amma ace babu ta inda yake samun relief daga gareta, kinsan Allah tsoron Allah nema ya mishi yawa amma da ba haka ba. Yadda muke a ƙasar nan ta Nasara da ba sai dai ya riƙa leƙa gidan karuwai ba, wasuma fa kina kallo da matan nasu har biyu ko fi ma amma suna bin matan banza. Kama haɓa Fatima tayi tare da jinjina kai Sannan tace "gaskiya ne fa wallahi, Allah dai ya duba yasa ta gyara" "Kima barni da ita zataci ƙwal ubanta ne, da kanta zata nemeshi idan taji wuya" Fatima zatayi magana Nawaz ta dawo, miƙa musu package ɗin tayi "gashi" Mazewa Maman sudeis tayi ta amshe Tare Da cewa gobe kisa ya kawoki gidana ki amshi wani magani, Nasan zai taimaka miki sosai, idan ma dai wani ciwon ke damunki ke koma aljanu ne duk Allah zai warkar miki dasu Idan kika fara sha" "To Nagode sosai, sai mun zo In'sha Allah " Fatima ce tace "Ni kuma inaga sai jibi idan mun haɗu a school" (Dayake Makarantar kwana hudu ce, monday zuwa Alhamis ne akeyi musu karatu, juma'a asabar da Lahadi kuma Babu, saboda masu zuwa wajejen Addini) "To Allah ya kaimu lafiya" cewar Nawaz tare da ɗaukar doguwar riga a Saman kujera tana sawa don ta rakasu zuwa ƙasa.. Koda ta raka su, wani me cab ne ya karaso kusa dasu ya gaishesu tare da cewa "Captain yace a kaiku duk Inda zakuje" Kallon Nawaz Maman sudeis tayi ta balla mata harara sannan tace "mijin marainiya kenan! Idan ya mutu lokacin zaki san meye duniya" Cikin motar suka shiga ita kuma ta koma ciki, zuciyarta fall tunani kala kala. Maman sudeis ce tace "driver kaimu Lacosté pharmacy" "Yes ma'am" drivern ya amsa. Dayake chemist ɗin beda nisa sosai cikin ƙasa da minti shabiyar suka kai, ce mai suka yi ya jirasu zasu siyo maganine. Koda suka shiga cikin pharmacy ɗin direct Wajen keeper suka wuce "don Allah maganin sha'awa nake nema (libido booster)" "Na ƙarawa ko na ragewa?" Keeper ɗin ya tambayeta "Na ƙarawa, inda halima inason me mugun ƙarfi ne" "Okay to Akwai duk kalar da kikeso" miƙewa yayi ya ƙarasa gurin canter ɗin dake zagaye da pharmacy ɗin. Wata madaidaiciyar roba ya ɗauko a gefen wasu magunguna ya mika mata. Dan duddubawa tayi sannan ta bashi kuɗinshi ya basu receipt suka fito. "Maman sudeis kada dai kice wannan shine maganin da kikace Nawaz tazo ta amsa gobe" Fatima tace tana zare ido. Basarwa maman sudeis tayi tare da cewa "shine mana, amma zan chanza mishi mazubi kuma zance kada ta bari oganta ya gani, ko akwai matsala ne" Kyalkyalewa da dariya Fatima tayi tare da cewa "zanso ace wata ƙawata me suna *Khadija Sunusi Lawal* amma *Seema* muke ce mata tana kusa, Wallahi da kinga tausayi, bazata bari a bata ba, cewa zatayi kada ki bata wai Allah zai tambayeki, kuma ma zata ƙara da cewa idan ke akayi miki haka fa? Amma da *Safiyyah Hassan (Ummi)* ce da Kinga dariyar mugunta, ai so zatayi ma taga yadda za'a ƙare idan tasha . "Ke Nifa yau ko *Yaya Muhammad Katsina* ne zaizo kasar nan bai isa ya hana naba Nawaz wannan maganinba" Maman sudeis tace suna shiga cikin motar. *A Chan Royal Shire Hotel........* Nawaz ce zaune ta rafka uban tagumi gaba ɗaya Abin duniya ya ishe ta, ta wani fannin su Maman sudeis gaskiya suka faɗa mata, domin a wannan ƙarnin da muke ciki babu namijin dazai zuba miki Ido ya kyakeki ba Tare da yayi miki wani abu ba, kuma ace kalau yake, balle Aayaan kowa ya kalleshi yaga lafiyayyen namiji meji da gwarzontaka. Hannun Aayaan da taji ya cire mata tagumine yasa ta dawo daga tunanin da takeyi "sannu da dawowa" tace a ɗan firgice "Bazan amsa ba sai kin faɗa min abinda yasaki wannan tunanin!" "Su Maman sudeis ce da Fatima suke fushi dani" "Lalala Gaskiya dole ki shiga damuwa, aminanki ne fa, ke kam me kika yi musu?" "Saboda Kai ne, amma pls kada ka tambayeni dalili yanzu, zan faɗa maka daga baya da kaina" "Okay to bazan tambayeki ba amma gobe zamu shirya muje mu basu haƙuri Koh" "Eh In'sha Allah, thank you" "Muje muyi wanka lokacin sallah ya kusa, inaso idan munyi Sallah zamuje wani park" Aayaan yace yana daukar Nawaz Tare da ɗaga ta sama. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *Zaria Nigeria......* Tuni Inna zuwairah ta koma gida domin hassu komai ya koma daidai, kuma Mummy batabar Sarfraz haka ba saida tasa family Doctor ɗinsu yaci mishi sannan kuma yayi mishi bayanai da yawa akan yadda ake bin mace, bawai da garajeba. Zamansu ya dawo dai dai gwanin sha'awa, don hatta da shaƙuwa sun ƙara fiye da tada, sai dai har yanzu hassu takanji fargaba idan taga ya nufota da bukatar shi. Duk kwana uku sai sunje gidan Mummy sun gaisheta inda itama Hassu ɗin a wannan Monday ɗin me zuwa Za'a maidata makaranta don har an samu tsohuwar da zata riƙa zama a gidan. SARFRAZ ba kunya gareshiba dama! don haka shima dagewa yakeyi akan sai hassu ta sake dashi fiye da Yadda suke a yanzu, duk maganar da tazo bakinshi ta Rashin kunya faɗa mata yakeyi, tun tana jin kunya wani zubin ma guduwa takeyi, to yanzu harta dena sai dai tayi Banza dashi. *Ta ɓangaren Umma kuwa* ta samu lafiya sosai sosai fiye da sanda fauziyya ke kula da ita, domin yanzu ummin Nawaz raba dare takeyi tana yin addu'oi a cikin Garin ganyen magarya da sassaƙenshi wanda take haɗa wa da zuma tana wanke mata ciwon dashi, kuma kullum gidan tsaff yake babu datti domin ciwon ma ya dena wari dalilin ganyen magaryar da ake sa mishi. Sannan ummin Nawaz ta gyarawa Jamila ɗakin Nawaz ta maida ita chan, sam bata bari kowa ya ganta, domin yanzu ma cikin ya daɗa fitowa sosai Kuma Gashi Yanzu ana Yawan zuwa gidan don ganin jikin umma. Ko gidan ka Shigo bazaka taɓa cewa akwai mara lafiya ba, Domin hatta da ɗakin umma kamshin turaren wuta yakeyi kala kala.. Ita kanta umman sau uku Ummin Nawaz take yi mata wanka, haka take kullum tsaff da ita, babu me cewa ma tana fama da wata lalura idan ba ƙafar ka gani ba. Abin duniya ya ishi umma, kullum cikin dare saitayi kuka ta godewa Allah, tana tuba zuwa ga Allah akan ya yafe mata sannan yasa idan ta roƙi ita Rahama ɗin da Nawaz suma su yafe mata, abinda take yi mata ko ɗan uwa wanda suka fito ciki ɗaya da ita yake yi mata tasan wata rana dole saiya nuna ƙosawa, amma ita sam bata nuna wata damuwa kullum ma ƙara zage damtse takeyi Mummyn Aayaan kam ganin ummin Nawaz bata komaba yasa itama tayi zamanta gidansu SARFRAZ, sai dai lokaci bayan Lokaci tana zuwa gidan su Nawaz ɗin su wuni Tare Da ummin Nawaz ɗin, Dalilin haka ne ma yasa ta Saba da Inna talatu sosai har zuwa gidanta ma yakeyi wani zubin itama tayi mata yini. *ENGLAND........* Da sassafe suka shirya don zuwa gidan maman sudeis, sosai Nawaz take farinciki Idan ta tuna Maman sudeis tace zata bata maganin dazai taimaka mata. Doguwar riga tasa baƙa Sannan ta yafa mayafinta, ita Aayaan yaba motar yace ta tuƙa su yanason yaga ko tana gane abinda yake koya mata (kusan sati ɗaya kenan daya fara koya mata motar, amma da dare suke fitowa saboda titin yafi rashin hayaniya) Mamaki sosai Aayaann yayi ganin yadda Nawaz ɗin take tuƙin a nutse, ƙarfin halinta yana matuƙar birgeshi matuƙa, kuma hakan yana ƙara sa tana birgeshi sosai. Har bakin kofar gidansu Maman sudeis ita ta tuƙa Sannan tayi parking, shikuwa Aayaan daɗi ne Kamar zai kashe shi, sai tafa mata yakeyi yana cewa good job my extraordinary wife. Zama yayi a waje ya jirata bayan ya bata kayan daya saba haɗowa sudeis yace takai mishi saita kawo mishi sudeis ɗin ya tayashi hira. Aikam sunsha hira ita da Maman sudeis kamar basu bane suka rabu jiya cikin ɓacin rai, koda zata tafi haka ta ɗauko mata maganin bayan ta canza mishi roba tace mata ta riƙa shan guda biyu da safe, biyu da rana, biyu da yammah.. Godiya sosai Nawaz tayi mata tare dayi mata Alƙawarin zata riƙa sha kullum. Lokacin da Maman sudeis ta rako Nawaz ne Aayaann yake ce mata "mun tuba a yafe mana, bazamu kuma ba duk da bamusan laifin da mukayi ba" Dariya tayi tace mishi " Babu komai ai an yafe muku, sai dai ku kiyaye gaba.. Koda zasu koma gida ita ta tuƙa su har bakin hotel ɗin su. Bayan sunje gida ne Nawaz ta samu guri ta ɓoye maganin inda Aayaan bazai ganiba kamar yadda Maman sudeis ta buƙata, amma saida tasha guda biyu. Ranar monday da kyar Nawaz ta yarda taje makaranta saboda wata iriyar muguwar kasala da take damunta, ga yawan mutuwar jiki kuma bini bini tayita hamma. Koda taje Makarantar ma babu Abinda ta iya tsinanawa inbanda kwanciya da tayi a saman desk, tayi hamma tare da miƙa yafi sau hamsin, itafa Bama ta gane me ake koya musu sam. Ita kuma Fatima na ankare da ita, sai dai bini bini ta Kalli maman sudeis ta tuntsire da dariya. Tsabar Yadda take dariya saida hankalin lecturer ɗin yakai kanta, ai kuwa take yace *"Fatima Ibrahim Magume* stand up" Miƙewa tayi tana raba ido, "why are you laughing" lecturer ya tambayeta Sunne kai tayi tare da cewa "I'm sorry sir" "Okay sit down but try to control your laughter coz u are disturbing others" "Okay sir thank you" komawa tayi ta zauna amma idonta nakan Nawaz wadda tayi shandar shandar a saman desk kamar wadda take laulayin ciki. Gaba ɗaya Nawaz ba'a cikin hayyacinta take ba, tun jiya takejin sauyi a jikinta gashi batasan Dalili ba, ko ganin Aayaan tayi sai taji ta fara yoyo, a jiya saida ta chanza pant yafi sau goma. Ga wani irin mugun feelings ɗin da batasan irinshiba da yake damunta, a yanzu fa ko son ganin Aayaan ɗin ma batayi balle ace ya taɓa ta, don yana tabata jikinta ke mutuwa duk ta daburce, taji gaba ɗaya shi kawai take buƙata, kuma ita ba iya faɗa mishi zatayi ba, haka jiyan da dare dakyar ta iya yin Barci saboda feelings, Yadda takeji kamar ka turmushe Aayann ɗin da kanta. Yanzu haka a Cikin zuciyarta addu'a takeyi akan Allah yasa ba alhakin Aayaan bane ya kamata saboda fa ita abin ya fara Wuce tunaninta, domin yanzu haka pant ɗinta jiƙe yake sharkaf har damunta yakeyi, kuma duk hakan ta faru ne Saboda Aayaan data tuna. Ƙosawa tayi a tashi saboda taje gida, gaba ɗaya yanzu tunaninta be wuce Yadda zata cigaba da zama a haka ba, tunanin Yadda dare zai risketa yauma takeyi, domin Abin na yau har ya Wuce na jiya ....... *Anya Maman sudeis kin kyautawa Nawaz kuwa*😆🤭🤣🤣🤣🤣 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *72* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* To *Barrister Maryam Ibrahim Aliyu (Autar mama)* ga naki shafin, fatan dai za'a bar Nuwairah (Chu-chu) ta karanta ❤️ Kamar kullum yauma dai wajen ƙarfe uku da rabi lecturer ɗin ya fita ya basu guri don su tattauna, yana fita Fatima ta koma kusa da Nawaz ta zauna "Sis wai meke damunki ne? Tun ɗazu na lura bakida lafiya" Hamma ce ta kama Nawaz mai ƙarfin gaske hatta idonta saida ya cika da hawaye, saida ta gama hammar sannan tace "wallahi sis bansan meke damuna ba sam, gaba ɗaya dai jikina a mace yake kuma babu Abinda nake so kamar na kwanta" "Ayyyah sannu! Ko zaki kira ogane kawai yazo ya maidake gida?" Shiru Nawaz tayi, a zahirin Gaskiya tanaso taga Aayaan kuma tanaso taje gida, to amma idan ta ganshi tasan Abinda takeji game dashi ƙaruwa zaiyi "mtsewwwss Kawai bari a tashi" Cewar Nawaz tanayin wata uwar miƙa kamar macijiya, babu inda be juya ba ajikinta, wata hammar ce ta kuma zuwa mata, da sauri tasa hannu ta rufe bakinta. "Anya kuwa Madinah! nifa na fara zargin ko dai ciki gareki! Wannan hamma haka da kasala!" Cewar maman sudeis wadda a lokacin ta ƙaraso gurinsu Kallonta Nawaz tayi tace "Maman sudeis aida cikin ne ma Ni sainafi kowa farinciki" " Hmm kin daiji dashi" Maman sudeis tace tana zama gefen Fatima. Amsar sudeis Nawaz tayi tana mishi wasa amma sam zuciyarta taƙi barinta ta huta da tunani "Madinah yaushe kike ganin zaku koma Nigeria?" Fatimah ta tambayi Nawaz "Inaga nan da wata Uku ko huɗu, Amma dai sai yadda ta kama saboda colonel Zai iya nemanshi ko yaushe Idan wata ukun daya dauka na hutu suka ƙare" "La kice ma Duk Kusan Lokaci ɗaya zamu koma!" Cewar maman sudeis tana murmushi "Ai kam dai Nima inaga duk Kusan hakan zamu tafi" Fatima tace tana miƙewa "bari na samo ruwa in dawo" Itama Nawaz Sai ta mike tare da saɓa sudeis a Saman kafaɗarta "muje mu raka ki mana" Tare suka ƙarasa gurin mai ruwan, roba ɗaya Kowa ya ɗauka Sannan suka samu guri a bakin shagon suka zauna, hira sukeyi sama-sama Inda suka hango motar Aayaan ta tunkaro su. Koda ya karaso Nawaz ji tayi Kamar an ninka abinda takeji ne sau goma, domin yayi matuƙar yin kyau cikin wasu ƙananun kaya ƙirar kampanin Armani, rigar Royal blue ce mai v neck sai wandon baƙi slim fit me kyau, tsaff suka fito da duka ƙirar jikinshi musamman damatsanshi, ta cikin rigar ma idan ka kula da kyau kana iya hango curarren ƙirjinshi da six packs ɗin cikinshi. Har sabon gyaran fuska yayi kuma Fuskarshi cike take da walwala, da murmushi ya ƙarasa kusa dasu inda ya duƙa saitin Nawaz cikin siririyar muryar masoya yace "honey ya jikin naki" sannan yasa hannu ya amshi sudeis tare da kara shi a ƙirjinshi. Gaishe shi su Maman sudeis sukayi kamar yadda suka saba Sannan yayi gaba zuwa mota amma duka hankalinshi yana kan Nawaz, don Idan idonshi ba ƙarya yayi mishi ba yaga kamar ta rame kaɗan. Nawaz dai matse cinyarta tayi Sannan tanajin kamar ta zunduma ihu "Ya ilahi na roƙeka ka taimaka ka kawomin agaji" abinda Nawaz ke furtawa a Cikin zuciyarta kenan. Koda suka shiga cikin motar ma Nawaz rufe idonta tayi ta kwanta cikin seat ɗinta, gaba ɗaya kamshin Aayaan ya isheta, ji take kamar ta rungumeshi ta cusa kanta Cikin ƙirjinshi kila ta samu relief ɗin Abinda takeji, sai dai kash bazata iya yin hakan ba saboda tsananin kunyarta. Tanaji duk suka tafi gidansu amma ko ido ta kasa buɗewa suyi sallama "dear wai me ke damun kine?" Dama jira takeyi sai ta fashe mishi da kuka. "Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, sweetheart meya faru" babu shiri yayi Parking ɗin motar a gefen titi Sannan ya fito ya koma gefenta, ɗaukarta yayi ya rungume ta a ƙirjinshi sai ya zauna a seat ɗinta Sannan ya ɗora ta a saman cinyarshi. "Rungumeshi tayi ta cusa kanta a ƙirjinshi tana shaƙar daddaɗan kamshin turarenshi wanda ya gauraya da kamshin jikinshi ya bada wani irin kamshi me shiga zuciya. "Sweetheart pls meke damunki? Ko ina cutar dake ne?" Shiru Nawaz tayi tana sauke ajiyar zuciya akai-akai "Ki kulani mana pls" Cikin kasalalliyar murya Nawaz tace "banida lafiya ne kuma bansan meke damuna ba" "Zaki iya faɗamin yadda kikeji a jikin ki? Ɗaga mishi kai tayi alamar "Eh" "Okay to inaji faɗa min" A cikin sanyin jiki ta fara magana "kaga inajin kasala, ga yawan hamma dason jin inyi barci, ga damuwa da tayi min yawa". Tunawa Nawaz tayi cewa shifa likita ne, tasan Dole zai gane sha'awa ke ɗawainiya da ita, ai kam da sauri ta ƙara da cewa "sannan bayana yanamin ciwo, kaina ma kamar zai fashe, kuma inajin jiri" A farko Aayaan harya Fara murna cewa Nawaz ta zama Yar hannu kenan zasuyi Amarcinsu a daɗin rai, sai kuma yaji ta sako wasu ciwukan kuma. Shiri yayi yana Nazarin to wannan wane Irin ciwo ne? "Dear mu Wuce Asibiti daganan" " Ni bazani Asibiti ba, ka kaini gida kawai" cewar Nawaz don tasan asirinta zai iya tonuwa idan har akaje Asibitin. Da ita rungume a ƙirjinshi ya koma side ɗin driver, wani irin bahagon tuƙi yayi domin tana saman cinyarshi rungume a ƙirjinshi yake driving ɗin har suka isa gida. A Saman sofa ɗin dake falour ya kwantar da Ita tare da shiga ɗaya bedroom ɗin yana ɗauko First aid kit, jininta ya gwada yaga ya ɗan yi sama kaɗan, sai heartbeat ɗinta shima ya ƙaru saidai kuma temperature ɗin jikinta normal ne. Duk tasashi a tension, ya kasa gane meke damunta, shidai yasan babu sauro garin balle yace ko malaria ke damun ta, and kuma basu taɓa yin sex ba balle yace ko laulayin ciki takeyi. Shiru yayi Domin kanshi ma Neman bugawa yakeyi, a ganinshi dole aje Asibitin gashi kuma tace ita bataso aje, and kuma shi bayason ɓacin ranta. "To yanzu me zakici?" Aayaan ya tambayeta yana kallonta in a pity face domin wani Irin mugun tausayinta yakeji a cikin zuciyarshi da ruhin shi. "Tea Kawai amma kasa min lemon grass sosai" "Okay to an gama ranki ya daɗe" tashi yayi ya shiga kitchen da sauri don haɗa mata. Itama tashi tayi ta shiga bedroom, drawer da Maman sudeis ta ciro magungunan nan ta buɗe da nufin ta ɗauko itama tasha tasan zata samu relief tunda dai sunce na kashe sha'awa ne, and kuma abinda ke damunta kenan, Amma abin mamaki babu ko ɗaya, ko empty robar ma babu. Dafa kanta tayi tare da cewa "ya ilahi ka yafe min badon halina ba, zuwa Yanzu na gane cewa alhakin bawan ka dana ɗauka ne ya hanani sukuni yanzu, wallahi bansan cewa haka yaya Aayaann yake jiba idan ya ganni sai yanzu da hakan ta faru dani, Na tuba! Na tuba!! Na tuba!!!" Saman gado tahau ta kwanta tayi flat tana kallon ceiling, tunani takeyi taya zata faɗawa Aayaan damuwarta, tasan idan yaji hakan ma shi daɗi zaiji amma ita batasan ta inda zata soma ba. Haka suka kwana babu daɗi, gaba ɗaya Aayaann ya rasa yadda zaiyi, koda safiya tayi haka ta tashi jikinta yayi zafi rau kuma idonta ma duk ya faɗa gashi yayi fari tarr. A daddafe yau ɗin ma taje Makarantar, batason zama a gidan tare da shi Saboda rasa sukuni takeyi kuma ba relief zata iya samu ba tunda bata bari yasan damuwarta ba. Haka ma dai yau ɗin ma babu Abinda ta iya ganewa har gara jiya, Fatima kam tausayi Nawaz ɗin ta fara bata Saboda yadda taga ta koma Kamar ba ita ba, ita kuwa maman sudeis ko ka ƙasan takalminta. In takaice zance dai yau sati ɗaya da fara shan maganin Nawaz, gaba ɗaya ta zama kamar ba ita ba, kowa ya ganta sai yasan tana cikin damuwa gashi har faɗawa tayi kuma ta ƙara haske tayi fari fat, cikin wani ikon Allah kuma ko da wasa bata taɓa kawo cewa maganin da take sha bane yakesa take jin wannan sabon yayayin ba. Yauma dai zaune suke babu makaranta, gaba ɗaya shima Aayaann ɗin baya cikin hayyacinshi, damuwar da yake ciki tasa ko sha'awar Nawaz ɗin ma bayayi, yanzu burinshi Kawai ta samu Lafiya taci gaba da walwalar da takeyi kamar da. "Plssss sweetheart ki faɗa min ko gida kikeso na kaiki?" Girgiza kai Nawaz tayi Alamun "A'a" "To ki faɗa min meke damunki pls" "Fashewa tayi da kuka domin dama Yanzu sun ƙulla amintaka ita da kuka, domin magana ɗaya ata biyu sai tayi kuka, Ni Bansan meke damuna ba, ko mutuwa zanyi ne" "Babu shiri Aayaan ya rufe mata baki tare da cewa "Stop it! Idan baso kikeyi Ni na mutu kafin ke ki mutu ɗin ba" "Zakije gidansu haidar abokina inda su hassu suka sauka lokacin da SARFRAZ beda lafiya?" "Gyada kai Nawaz tayi alamun Eh" "Okay to bari in shirya mu, sai inyi driving ɗinmu, tafiyar awa ɗaya da rabi ce a Mota" Tsaff ya sirya cikin farar jallabiya ita kuma baƙar Arabian Abaya, tayi kyau sosai sai dai fuskarta a cunkushe take babu fara'a. Sosai yake ƙoƙarin yimata hira sanda yake driving ɗin saboda ya rage mata damuwar da take ciki amma babu wani improvement da aka samu. Wurin ƙarfe ɗaya saura suka isa gidan haidar, murna gurin Madam haidar ba'a magana, rasa inda zata sasu tayi, haka ta dage ta cika musu gabansu da Kayan ciye ciye, inda daga baya kuma hirar su SARFRAZ ta ɓarke tsakanin su. Labarin Yadda aka riƙa drama da SARFRAZ sanda beda lafiya haidar yake ba Nawaz. Dayake Lokacin shan maganinta yayi kuma bata shaba sai taji abubuwan da takeji sun ragun mata sosai, hakan yasa ta saki jiki sunata hira. Sosai Aayaann yake ta jin daɗi Yadda yaga ta ware sosai, shi a nashi beƙi kullum ya kawo taba har dai zata riƙa samun sukuni irin haka. Sai gurin ƙarfe takwas saura Aayaann yace zasu tafi, aikam haidar yasa Madam Ɗinshi ta kawo musu tea yace su fara sha tukuna sai su tafi saboda Kada barci ya kamashi suna hanya gashi akwai ɗan nisa.. Nawaz dai bata sha ba sai Aayaan daya ɗauki mug ɗaya yashanye. Har gaban mota suka raka su sannan suka koma gida bayan Aayaan ya ɗauki hanya. Dariyar mugunta haidar yaketa yi bayan su Aayaann sun tafi, mugunta ya haɗa wa Aayaan a cikin shayin Nan, domin desire tablet ya zuba mishi a ciki har guda huɗu dayake tasteless ne kuma colourless, mai uban ƙarfi ya zuba mishi wanda idan ba kwanciya da Mace kayi ba to saikayi sati ɗaya kana ciwo. Waishi ya rama ne saboda shima randa yayi Aure haka suka haɗa baki da Farouk suka Zuba mishi, gashi kuma ranar Amarya tana al'ada, ba ƙaramar wuya yasha ba A speed sosai Aayaann yaja motar, inda ƙarfe tara da ƴan mintoci suka isa gida, ai kuwa kamar tsafi yana saka kafarshi a cikin falour yaji mararshi ta ƙulle ga wani uban sanyi daya fara ji lokaci daya Kuma duk tsigar jikinshi sun bubbuɗe, durƙushewa yayi a gurin saboda ko ƙafarshi ya kasa ɗagawa, tabbas yasan wannan sharrin haidar ne saboda dama ya rantse shima sai ya rama Abinda sukayi mishi wata rana, yanzu ta zaiyi kenan? Gashi Nawaz ba lafiya gareta ba sannan ga Alƙawarin dayayi Mata na cewa bazaiyi mata dole ba. Yauma dai babu yawa, Amin uzuri nayi baƙi ne *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *73* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Tsoro ne ya kama Nawaz ganin Aayaan durkushe yanata faman zufa bayan kuma sanyi akeyi a garin, da sauri ta ƙaraso kusa dashi, kama mishi damtsen hannunshi na dama tayi wanda tafinta ko rabi be ritsaba "yaya meya sameka? Yanzunnan fa muke Lafiya dakai" Sosai yakejin jiki, cikin minti uku amma nema yake ya fice daga hayyacinshi "samo min ruwa mara sanyi sannan kije cikin drawer ta Biyar Akwai Wani magani ki kawo Min Yanzu pls" Da sauri Nawaz ta dauko Ruwan Sannan ta shiga dakin ta duba drawer, babu maganin data gani a ciki Sam Da sauri ta dawo tare da bashi Ruwan kuma tana cewa "yaya banga maganinba fa kwata kwata, koba a cikin drawer yake ba? Runtse idonshi Kawai yayi tare da cije laɓɓansa na ƙasa, shi kaɗai yasan Abinda yake ji. Rungumeshi Nawaz tayi tana cewa "yaya don Allah meke damun ka? Pls ka faɗa min" Idonshi wanda ya chanza kala yayi jajir ya buɗe ƙasa ƙasa yana kallonta, tausayinta ne ya kama shi Domin yasan idan ya chafketa Abin bazai yi Mata kyau ba, jijiyoyin da suka fito a saman goshinshi take taɓa wa tana cewa "ko ciwon kaine ke damun ka? Cikin wata iriyar murya Wadda saida Nawaz ta ɗago ta kalleshi da kyau donta tabbatar cewa shi yayi Maganar yace "ciro wayata a aljihu kiyi min dialling ɗin wata Number zakiga an rubuta Bestie haidar a jiki" Dubawa tayi tai dialling sannan ta miƙa mishi wayar, aikam kiran yana fara shiga haidar ya ɗaga yana tuntsira dariyar mugunta "Ai dama zaman jiran kiranka nakeyi domin Nasan dole ka kira" Kallon Nawaz Aayaan yayi yace "pls kije kitchen ki dafa min mint tea" "To" Nawaz tace sannan ta miƙe da sauri ta nufi kitchen, shifa bawai shan tea ɗin zaiyi ba Kawai ya kore tane saboda ya samu damar yiwa haidar magana. "Haidar meka zuba min a cikin tea ɗin daka bani ɗazu?" Tuntsirewa haidar ya karayi da dariya Sannan yace "Irin maganin da kuka zubamin a cikin drinks Ranar da aka ɗaura min aure, Ammafa kai guda huɗu na zuba maka saboda dama Bahaushe yace Ramuwar gayyah tafi ta gayyah zafi" Cikin Wata irin murya me ƙaraji Aayaan yace "Wallahi haidar na rantse da Allah idan kasa na kashe Yar mutane ko nayi mata wani lahani to wallahi kaima sainazo na harbe ka sai dai duk Abinda zai faru ya faru daga baya, amma ya za'ayi ka zuba min kwaya har guda huɗu bayan Kasan Guda ɗaya akesha itamma ga wanda ke fama da ciwon Rashin sha'awa, kuma ka fa san Irin karfin sha'awa ta koda babu magani" "Oho Ni sanda kuka zubamin meyasa bakuyi tunanin kada na kashe ƴar mutane ba Nima?" "Haidar pls keep joke apart wallahi Nawaz is still Virgin banaso naje nayi abin da za'a dawo ana da an sani saboda tun yanzu I'm loosing control of my self" "Innalillahi wa'inna alaihi raji'un! Subhanallah, wallahi bansaniba da bazan zuba maka ba, Amma abokina me kake yi har zuwa yanzu baku zama intimate ba?" "It's my personal issue, yanzu dai koda kasheta nayi nasan iya wayarnan da mukayi ta Isa shaidar cewa kaine sila saboda nayi recording ɗin duka maganganun da mukayi", be jira jin Amsar da haidar zai bashi ba ya yanke kiran tare da kashe wayar gaba ɗaya yana jefata saman kujera. A daddafe ya ƙokarta ya miƙe yana runtse idonshi saboda Yadda yakejin mararshi tana chure mishi ga wani irin zugi da take Yi mishi, length Dinshi kuwa zuwa wannan lokacin ya koma Kamar katako, da kyar ya samu ya isa bedroom ɗinsu, ai yana shiga yayi flat a saman gado yana sauke numfashi a wahale "Allah sainaci uban haidar duk randa muka haɗu, Meye Nashi nayimin irin wannan aika aikar?" 🤭🤭🤭 Hajiya Nawaz ana chan an zage ana dafawa miji shayi, har ta juye a cikin teapot ta ɗauki mug zata fito ta tuna da cewa yaufa tun safe batasha maganintaba Gashi tayiwa maman sudeis Alƙawarin cewa duk rintsi kullum zatasha, a cikin drawer kitchen ɗin dama ta ɓoye, ai kuwa cirowa tayi tana tunanin guda nawa zatasha tunda batasha na rana ba, a maimakon tasha guda biyu sai kawai tasha guda uku sannan ta ɗauki tea ɗin ta fita zuwa falour, ganin baya falour yasa tayi bedroom ɗin da sauri, a kwance ɗai-ɗai ta sameshi harya cire jallabiyar jikinshi, that means daga shi sai best da dogon wando. "Yaya ga tea ɗin" Nawaz tace tana kallon murɗaɗɗen jikinshi da yake cike da kwantattun Gashi. "Sweetheart bazan iya shan tea ɗin nan ba yanzu, pls just get on the bed " Saman gadon ta hau Sannan ta haye saman faffaɗan ƙirjin shi tare da lumshe ido, hannunshi yasa yana patting ɗin bayanta tare da cewa "sweetheart ya jikinki?" Mamaki Abin yaba Nawaz, ji yadda yake jin jiki amma kuma wai bata kanshi yakeyiba ta ita yakeyi bayan ita nata be kai nashi ba, "Yaya kaine fa kakejin jiki Yanzu, Ni na samu sauƙi" "At least aini nasan meke damuna, Amma kinga ke fa bansan meke damun kiba kuma kin ƙi bari muje Asibiti balle in duba ki da manyan na'urori". Zuwa wannan lokacin Nawaz ta fara jin feelings ɗin na dawo mata kaɗan kaɗan, amma gani takeyi kodon ta kusance shi sosai ne, tunda tayi male-male a Saman ƙirjinshi kuma sai patting ɗin bayanta yakeyi. "Yaya meke damunka?" "No need kisan meke damuna tunda Nasan ba magani zan samu ba, kuma Nima Na riga da nayiwa kaina Alkawari balle ince zan nemarwa kaina mafita koda da ƙarfin tuwo ne" "Pls ka faɗa min wallahi i will help" "Kinyi Alkawari " Da sauri Nawaz ta ɗaga kanta Tare da cewa "wallahi nayi, just faɗi ko menene" Beso Nawaz ta rantse da wuri ba daboda yasan da kamar wuya *Wai gurguwa da Auren nesa* amma bari ya faɗa mata yaga me zatayi "Ke nake buƙata, bawai tsurar keba! Dukanki da kuma abu Mafi muhimmanci a rayuwarki Wanda sanadin kare martabar shi Saida kika kusa yin kisa, i want us to be intimate! Mu zama Abu ɗaya bawai a baki ba hatta a zahiri, amma fa saida Amincewar ki" Wani miyau tsinkakke Nawaz ta haɗiye, lallai maza babu ruwansu, ita kwananta nawa tana fama amma ta kasa faɗa mishi damuwarta sai gashi shi freely ya faɗa mata tashi, lallai Aayaan na musamman ne bayada Nuƙu-nuƙu sam, itama zuwa yanzu tana buƙatar mijinta gashi dama maganin maman sudeis ya soma aiki, ita a Wajen tama gani takeyi kamar Allah ne ya kawo mata damar da tafi sati tana nemanta cikin sauƙi. Jin Nawaz ɗin tayi shiru bata ce komai ba yasa Aayaan jin wani iri a cikin zuciyarshi, tunda yake be taɓa yin negative though akanta ba sam amma a yanzu saida yaji a cikin zuciyar shi cewa Anya kuwa Akwai Ranar da Nawaz zata ƙaunaceshi? Ya daɗe yana yi mata uzuri amma meyasa ita ko sau ɗaya bazata yi mishi ba?" Kamar daga sama yaji Nawaz tace "I'm all yours kuma ko me kayi niyyar yi dani kayi na baka dama, to meye ma amfanin yin auran namu tunda bazamu iya cire juna a cikin damuwa ba? And kuma ina neman yafiya a gareka na wahalar da kai da naketa yi akan haƙƙin ka, don Allah kayi hakuri ka yafe min wallahi nayi maka alƙawarin bazan kuma ba" Ɗagota yayi daga jikinshi sannan ya tashi zaune, kallonta yakeyi kamar be taɓa Ganin taba "sweetheart kece kikayi magana yanzu ko kuma kunnena ne yakemin gizo? Murmushi Nawaz tayi tare da cewa "Nice nayi ba kunnenka bane, cewa nayi Ni taka ce dama kuma kayi duk Abinda kaga dama dani, kuma ina roƙonka daka yafemin cutar dakai da nayi tayi saboda nawa son zuciyar mara Amfani" Farinciki ne da murna suka kama Aayaan lokaci ɗaya, ji yake kamar ya ɗauki Nawaz ya haɗiye ta ya huta "dama akwai ranar da zata ƙaunaceshi kamar haka? Lallai mahaƙurci mawadaci." Janyota yayi ta faɗo jikinshi Sannan yayi hugging ɗinta sosai, Magana ya fara yi a hankali kuma cike da bata kwarin gwiwa "Sweetheart i promise you I Will be extra gentle, and kuma kema inaso ki fito da wannan jarumtar taki yau zatayi mana Amfani, kuma ki cire duka kunyarki ki ajiyeta a gefe gobe da safe sai ki mayar" Ita dai Nawaz lafewa tayi a jikinshi tana shaƙar kamshin jikinshi, gaba ɗaya maganin ya soma aiki gadan gadan, hakan nema yasa jikinta ya mutu gaba ɗaya. Miƙewa Aayaan yayi Sannan ya ɗauketa in a bridal Way "zo muje kiga wani surprise, it's for you alone" A gefen store dama akwai wata ƙofa, ita ya nufa ɗauke da Nawaz a hannunshi, dayake Nawaz ɗin bata da bin ƙwaƙwafi bata taɓa tambayarshi ƙofar ina bace. Buɗe ƙofar yayi ya shiga ciki amma sai dai ba'a iya ganin komai saboda duhu, switch ya taɓa ya kunna, aikam wani irin haske ne ya gauraye ɗakin, babu irin kalar bulb ɗin da babu a ɗakin bayan cikashi da akayi da party lights. Nawaz da kanta ta bukaci ya sauketa saboda ta samu damar ƙarewa ɗakin kallo, komai na dakin Golden colour ne sai ɗan ratsin fari a inda ba'a rasa ba. Babban gadone design ɗin Italy girmanshi har yayi yawa, kowane bango na ɗakin photon Nawaz ne tana barci, iya carpet ɗin dake kasan ɗakin ya isa abin kallo, saboda kana takawa kafarka zata nutse a ciki, ta kowace kusurwa kuwa wasu irin crystal glasses ne kamar diamond suna haske, duk da girman gadon da wardrobe ɗinshi da side drawers din amma ɗakin wargajeje, zaka iya rugawa da gudu ma, Frame's ɗin dataga an ƙawata ɗakin dasu ta tsaya tana kallo, love quotes ne rubuce a jiki suma suna haske kuma a jikin ko wanne sai an rubuta *_NAWAZ AND AAYAANN ✓ FOREVER LOVERS_* Zanin gadon kanshi wasu rubutu ne a jiki ƙananu kuma da alamu tare aka saka shi dasu, data ƙura ido sai taga ashe *Nawaz and Aayaan* aka rubuta cikin style ɗin heart. Daɗi ya cika Nawaz rasa me zata yi ma tayi, sai kawai ta daka tsalle ta maƙale wa Aayaan Tare Da cewa "I LOVE YOU" Kamar mutum mutumi haka Aayaan ya koma, shikam dai wannan juma'ar da wace Irin Sa'a tazo mishi ne? Ace wai yau shine tsaye a gaban Nawaz har ta furta mishi cewa *She love's him* Rungume ta yayi da karfi Kamar zai maida ita cikin ƙirjinshi har saida tayi ƴar ƙara kaɗan Sannan ya sassauta mata rungumar" Wayar tafi da gidanka dake saman chest drawer ya ɗauka tare dayin dialling Number reception Inda yace a kawo mishi ko wace kalar nau'in kaza da suka girka yau sai kalolin Madara suma. *Ni kam matar Rasheed cewa nayi bari na leka Zaria kafin a kawo wa Aayaan kajin, nasan zuwa lokacin na dawo* *DON ALLAH MASU TSALLAKE ZARIA YAU KU TAIMAKA MIN KADA KU TSALLAKE DOMIN IDAN KUKA TSALLAKE NA YAU BAZAKU TAƁA GANE ME LITTAFIN SARFRAZ YA ƘUNSA BA, SABODA KADDARAR KOMAI TANA CIKIN NA YAU NE, NAGODE 🙏🙏🙏* *ZARIA NIGERIA.........* A firgice umma ta tashi daga barcin data fara wanda bazata wuce minti Talatin da fara Shiba, gaba ɗaya jikinta rawa yake yi Dalilin marfarkin datayi yanzu, "Fauziyya! Fauziyya!! Fauziyyah!!! Umma ke ƙwalawa Fauziyyah kira, wadda itama yau a gidan zata kwana saboda mijinta yayi tafiya kuma ya yarje mata tazo nan ta kwana saboda dama yaranta suna wajen surukarta. Ganin fauziyyah tayi nisa sosai cikin barcin da takeyi yasa umma ta fara jan jikinta har saida ta sauka daga kan katifar ta nufi inda fauziyyah ke kwance, bubbuga cinyarta ta fara yi tana ci gaba da kiran sunan ta. A firgice fauziyyah ta tashi tana mutsika ido "umma wa ya kawoki nan? Menene?" "Tashi Fauziyyah barcin nan ba namu bane domin Allah ya nunamin abinda Ni sam nama manta ba aikata" "Umma me kika aikata da bazaki bari gari ya waye ba? Yanzu fa Kusan karfe 3:30am na dare ne, (saboda tazarar awannin dake Tsakanin Nigeria Da England) "Fauziyyah idan nace zan bari Saida safe to komai ma zai iya faruwa, don wannan lokacinne nake ganin zan fara yin Abin Alkhairi ga Nawaz " "To umma menene?" Fauziyyah ta tambayi umma cikin zaƙuwa "Fauziyyah Ni mahaifiyar kice, don haka bazan ɓoye miki komai ba saboda kin riga da kinsan halayena Marasa kyau, cigaba umma tayi da cewa "Fauziyyah gaskiya Allah yana sona da Rahmar shi, amma daba hakaba da tuni Mutane dayawa sun mutu sanadi na" "Umma ki faɗa min menene yake faruwa? Don Allah ki dena jamin rai" Cigaba umma tayi da cewa "in zaki tuna lokacin bikinki Abban ku yaso ya haɗa Auren Nawaz da naki Koh, to kinsan wani mashahurin me kuɗi ya samo mata, Ni kuma a Lokacin sai hassada ta kamani akan idan aka yi Auren Rahama zata huta ta Dalilin ta gashi kuma ke ba wani me kuɗi zaki auraba. To alokacin dama wata ƙawata kande tanaso na rakata wajen wani boka amma bayarabe ne, to da mukaje ne naji tana faɗawa bokan cewa tanaso ne a fasa Auren yarinyar kishiyarta da za'a yi, to sai bokan yace mata Gaskiya bazai yiwu a fasa ba dole sai anyi bikin. To alokacin ta shiga damuwa sosai saboda itama yarinyar me kuɗi ne zai Aure ta Gashi kuma ita yarta batada ko saurayi. Ganin tashiga damuwa yasa bokan yace mata Akwai hanya guda ɗaya, hanyar itace zai turawa yarinyar aljanu waɗanda zasusa bazata taɓa bari mijin ya kusance taɓa, Kinga kuwa babu wanda zai yarda da Hakan, idan kuma mijin yayi taurin kai yace zaisa mata karfi to kuwa duk randa ya sake yayi kwanciyar Auratayyah da ita ai kuwa sai dai wani bashiba. Jin hakan ba ƙaramin daɗi yayi wa kande ba, ta tambayeshi kuɗin aiki ya faɗa mata ta bashi muka dawo gida, to dayake dama sai an fara yin nasu bikin Kafin naku, aikuwa a Daren da aka kaita washegari akace mijin ya mutu, ita kuma yarinyar aka kamata, saida akasha fama sannan aka gane ba ita ta kashe shiba aka saketa daga baya. Nikuma ganin abin ya faru da gaske shine naje gurin bokan nace inaso nima yamin irin aikin a kan Nawaz , maƙudan kuɗaɗe ya tambaye Ni, aikuwa nabashi saboda lokacin idona ya rufe da hassada. To dazan tawo ne ya bani wasu kwai guda uku yace sune suke ɗauke da aikin, ɗaya zaisa mata baƙin jini, ɗaya kuma zai hana ayi Auren ta koda an samu miji, na ukun kuma shine koda ma anyi Auren mijin mutuwa zaiyi muddin ya kusanceta. To kinji makircin da nayi, wallahi sam na manta da nayi wannan mugun abin, sai yanzu Allah ya tuna min, kinga kuwa da ace lokacin nan dana sasu suyi mata fyaɗe da sun samu Sa'a sunyi mata fyaɗen da mutuwa zasuyi, gashi yanzu tayi Aure, tsorona ɗaya kada mijinta ya kusanceta ya mutu. "Kai umma wai yanzu kina nufin kicemin mijin Nawaz be taɓa kwanciya da ita ba?" "Fauziyyah kada ki raba ɗaya biyu, be taɓa ba, saboda nifa ganau ce ba jiyau ba a wannan Abin, don yayinyar nan yanzu haka aurenta uku kuma duka mazajen a Daren Aurensu suke mutuwa, in takaice miki zance dai yanzu taƙi auruwa. Kinga kuwa dole hankali na ya tashi kada inyi silar mutuwar bawan Allah, nauyin rai ya hau kaina, banda cikin Rahma da nasa akayita zubarwa saboda Kada ta kuma haihuwa. "Innalillahi wa'inna alaihi raji'un, yanzu umma duk kishi ne yasa hakan?, Don Allah umma ki dage da tuba kila Allah ya yafe miki" "Ba wannan ba fauziyyah, yanzufa mafarki nayi wai mijin Nawaz ɗin ya kusance ta harya mutu ita kuma an kamata ance za'a kasheta ta Hanyar rataya, tsoro nakeyi kada hakan ta faru, duk alhakin ransu a kaina zai rataya tunda nice silar komai, Ni yanzu uban zunuban ma dake kaina sun isheni ba saina ƙara wa kaina wasu ba" "To umma yanzu ya za'ayi?" "So nakeyi in faɗa Miki inda na binne ƙwayayan sai kije ki haƙosu ki fasa su duka" " Umma don Allah ki bari gari yayi haske mana!" "Fauziyyah ki duba darajar haihuwar ki da nayi kitaimakeni kije ki haƙe su, wallahi ji nakeyi kamar mafarkin nan danayi Allah ne ya turomin da saƙo, inajin idan ban fasa ƙwayayan nan ba komai zai iya faruwa zuwa gobe." " To umma faɗa min gurin da suke inje in haƙosu in fasa" "Yauwa fauziyyah Allah yayi miki albarka yasa ki gama da duniya Lafiya, kije bayi dai-dai dutsen da ake wanka akai, ki matsar dashi zakiga sashin sumunti, to shi zaki haƙe, idan kika cirosu ki tabbatar kin fasasu duka Don Allah." Miƙewa fauziyyah tayi tare da cewa "to" Sannan ta fita, a zahirin Gaskiya tsoro ne fal zuciyarta amma kodon chanjin data gani daga mahaifiyar ta zata daure ta haƙe ɗin. Store ta buɗe ta ɗauki digger Sannan ta wuce bayin, inda umma ta faɗa mata nan ta duba, ai kuwa tasha wahala kafin ta iske kwan cikin wani kwano mai murfi a cikin ramin, tana cirosu batayi wata-wata ba ta fasasu duka, take wani irin mugun wari ya cika bayin, maida ƙasar fauziyyah tayi ta cike ramin sannan ta ɗauki chocilarta data ajiye a gefe ta fito ta wanke hannu a famfo Sannan ta koma ɗaki. Umma sai shi mata albarka takeyi tana fatan Allah yasa ta gama da Duniya lafiya, sosai fauziyyah taji daɗin addu'ar da umma take tayi mata duk da tasha wuya. Itama umma sosai taji kamar an sauke mata wani uban nauyi ne a jikinta, Domin sakayau haka tajita, duk kusan rabi daga cikin damuwarta ta kau. *ENGLAND.........* Knocking Aayaan yaji, Alamun order ɗin dayayi sun iso, kwantar da Nawaz yayi a gefen gadon tare da cewa "sweetheart ki jirani Anan I'm coming" Rufe ido tayi ba tare data ce komai ba. A Cikin wani Babban picnic basket aka shirya komai, amsa yayi ta koma ɗakin tare da ɗora basket ɗin a saman table ɗin dake gefen two sitters sofa ɗin dake ajiye a cikin bedroom ɗin, "Sweetheart tashi muci abinci" Zuwa wannan lokacin gaba ɗaya jikin Nawaz yayi weak da yawa, don haka bata iya tashi ba Saida ya ɗaga ta da kanshi, naman yayi ta bata, saida ya tabbatar ta ɗan ci da yawa Sannan ya buɗe robar Madarar ya kafa mata a bakinta, itama saida ta sha kusan rabi da quarter sannan ya cire robar a bakinta. Maida ita yayi ya kwantar shima ya ɗan rori Abinda zai rora yaci, Sannan yasha madarar shima, kauda kayan yayi jefe inda ya miƙe tare da danna wani madanni, aikuwa take wata kofar glass ta zuge, Ashe wani irin shu'umin bayi ne a ciki, komai yaji basaina tsaya bayani ba. Babban jacuzzi ɗin ya cika da Ruwan zafi bayan ya zuba bathing fragrances kala-kala acikin ruwan, tuni kamshi ya cika bayin. Komawa yayi ya cirewa Nawaz kayan jikinta Sannan ya cire nashi, ɗaukarta yayi ya koma bayin Tare yayi musu masauki a cikin ruwan daya haɗa, luff Nawaz tayi cikin ruwan domin ba ƙaramin ratsata yakeyi ba, sosai ruwan yake yi mata daɗi, Saida sukayi kusan minti goma a cikin ruwan bayan yayi mata brush shima yayi Sannan ya haɗa musu wani ruwan inda yayi nashi wankan, daga baya kuma ya yiwa Nawaz nata, towel ya daura a ƙugun shi sannan ya ciro wani ya nannade Nawaz a ciki ya fita daga bayin. A saman gadon ya ɗora ta tare da tsane mata ruwan jikinta duka sannan ya samu lotion me daɗin kamshi ya shafa mata, Nawaz tanajin duk Abinda yakeyi amma babu halin hanashi illa idonta kawai data rufe. Saida ya gama shiryata tsaff sannan yasa duvet ya rufeta, shima tsaff ya shirya kanshi Sannan ya maida towel ɗin ya daura tare da fita zuwa ɗaya bedroom ɗin, jallabiya ya ɗauka a cikin nashi kayan sannan ita kuma ya ɗaukar mata Babban mayafi da doguwar riga Sannan ya koma zuwa dakin. Sa mata rigar yayi tare da naɗa mata mayafin sannan shima ya zira tashi rigar, matsawa yayi Zuwa Babban carpet ɗin inda Yacewa Nawaz idan bazata iya yin sallar a tsaye ba zata iya zama. Juyawa yayi ya tada kabbara sannan ya fara karatun fatiha, tsabar ƙarfin hali irin Na Nawaz ƙin zama tayi, haka ta tsaya a tsaye gashi kuma jiri take gani kamar me. Raka'a biyu ya jasu sannan ya zauna ya fara zuba ruwan addu'oi, sosai yayi addu'oi iri iri inda daga bisani ya ɗora hannunshi a Saman kan Nawaz yayi wasu addu'oin. Murmushi yayi tare da cewa "ke Malama ce don haka Ni banada Abinda zan tambayeki don nasan duk Abinda zan tambayeki kin sani, yanzu ma abinda ya kamata shine in sa rana wacce zan riƙa ɗaukar karatu. Murmushi Saida yayi nasarar bayyana a fuskar Nawaz "haba yaya Aayaann Ni har na isa na koya maka karatu?, Babu ruwana gaskiya! Domin Nasan tsokanata kawai kakeyi amma ko kafarka ban kama a ilimi ba. "Oya to Yau zamu gani" cewar Aayaan tare da sunkutarta yana dorata a Saman gado Sannan yabita ya kwanta a kirjinta. " I know now you are ready right?" Runtse ido Nawaz tayi tana sauraron bugun zuciyarta daya haɗu da nashi "Idan kuma har yanzu you Are scared Shikenan zan iya haƙura" "Nop i am no More scared just somehow worried" "I promise to be extra gentle right? and in'sha Allah i will keep my words" Haɗe bakinsu yayi guri ɗaya ya Fara kissing ɗinta full of love and high feelings *Zan ɗauki hutu sai next month* saura inji kunce inyi haƙuri 🤨🤨🤨 🤣🤣🤣🤣🤣🤣 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *74* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* please🔞+, if not kuma kome Mutum yaji babu ruwana tunda dai na faɗa. Ita dai Nawaz addu'a takeyi aranta cewa "Allah yasa kada ta wahala kamar yadda hassu ta wahala, zuciyarta har fat fat takeyi idan ta tuna cewa Aayaan yafi Sarfraz girma ta kowace siga" Jin yana ƙoƙarin cire mata riga ne yasa ta fara mutsu mutsu , cire bakinshi yayi cikin nata tare da cewa "meya faru?" "Ni hasken ne yamin yawa" "Okay to Bari nasa dim light" Aayaan yace Tare Da miƙewa daga saman ƙirjin ta" Kashe duka bulbs ɗin yayi dama sauran duk wani haske dake ɗakin sannan ya ƙarasa side drawer ya kunna dim light, Be koma kan gadon ba saida ya zare rigar jikinshi, yayanin hasken ɗakin ba sosai bane, yayi kamar magrib ta sawo kaine, don haka Yana nufota ta lura babu kaya a jikinshi amma bata iya ganin jikin nashi sosai. Wani irin tsoro ne ya kamata ganin yayi mata wani mugun girma, rufe ido tayi tana cewa _"ya Allah ka taimakeni"_ Saida zuciyarta ta buga sanda taji saukar hannunshi yana ƙoƙarin cire mata riga, yana zare rigar ya haɗe ta da ƙirjin shi tare da janyo duvet yana rufesu. Kasancewar ya karanci Tsarin zubin halittar jikin ɗan Adam yasa sosai yasan erotic spots, bin duk inda yasan zai kashe mata jiki yayi yana wasa dashi, Hajiya Madina 🤭 kuwa ji tayi kamar ta zunduma ihu saboda yadda taji jikinta ya ɗauka, ji take kamar ana yi mata waiwayi, kamar kuma an zuba mata ƙwari sunayi mata yawo a jikinta Sannan tanajin marar ta kamar ta cika da fitsari. Sosai Aayaann ya maida hankali wajen wasa da sassan jikinta saboda yanaso ne HQ ɗinta yayi lubricating sosai yadda idan zai shigeta bazai ji mata ciwo ba, jikin Nawaz be fara vibrating ba Saida taji saukar bakinshi a saman kirjinta, Sannan ya riƙe ɗayan da hannun shi, harshen shi yasa yana wasa da nipples ɗin tare da sucking dinshi inda kuma yake massaging ɗin ɗayan da hannun shi, rawa jikin Nawaz ya ɗauka saboda wani irin Abu dataji yana tsirga mata a duka ilahirin jikinta, so take tace mishi abin yayi mata yawa ya bari amma ta kasa. Saida ya tabbatar ya kashe mata jiki ta hanyar wasa da boobs ɗinta Sannan ya koma yana bin duka sassan jikinta yana sumbata, ƙasan wuyanta da tsakiyar kirjinta, bayan kunnenta da cikin cibiyar ta. Sosai shima ya fita daga hayyacinshi Amma beso yayi introducing ɗin kanshi ba tare daya tabbatar jikinta na buƙata ba, shiyasa ya ɗaure har saiya tabbatar takai geji saboda so yake a yau ya tabbatar mata da Negative tunanin da takeyi akan sex ba gaskiya bane. Ƙasa yayi Inda ya ɗora bakinshi saman HQ ɗinta tare dasa harshen shi yana wasa da clit ɗinta, wani irin jan numfashi Nawaz tayi Sannan cikin wata irin sarƙaƙƙiyar murya tace "Nidai don Allah ya Isa haka, pls kayi abinda zakayi basai ka kashe ni ba" "Yea so nake na kasheki amma da hot pleasurable and high orgasms, i want you to cum more than million times" "Nidai don Allah ka bari, Wallahi numfashina so Yake ya ɗauke" Be kula taba illah ma himma daya ƙara akan sucking ɗin clit ɗin sannan yayi sama da hannuwanshi yana massaging ɗin boobs ɗinta softly. Fashewa Nawaz tayi da kuka domin shi kaɗai ne take ganin mafita a gareta, shikuwa wannan kukan da takeyi ba ƙaramar himma ta ƙara mishi ba, don Jin kukan yakeyi like she is moaning for more. Jin yana zira harshen shi cikin ramin HQ ɗinta yasa ta tsagaita kukan tare da ce mishi _"Nifa fitsari ya matseni, ka bari naje nayi sai in dawo"_ "Nop basai kinje ba just kiyi a cikin bakina dama ƙishi nakeji" A daidai lokacin ne wani irin precum ya Fara zubowa daga cikin HQ ɗin Nawaz me yawa, _"yea it's coming! I need more pls"_ Aayaan yace yana daɗa juya harshenshi a saman clit ɗinta _"Nidai ka sakeni inje in dawo, Allah zan dawo"_ "Nace kiyi abakina" cewar Aayaan yana maida bakinshi cikin ramin HQ ɗin tare da zuƙe duka precum ɗin, sosai yake wasa da clit ɗinta Inda ita kuma numfashinta ke neman shiɗewa saboda wani irin Abu dataji ya cushe mata a mara. _"Don Allah yaya Aayaann pls kabarni inje bayin"_ Yasan me takeji shiyasa be kula taba illah ma ƙara himma da yayi akan abinda yake yi, cire bakinshi yayi ya maye gurbin shi da yatsanshi manuniya inda ya fara mata penetration dashi, _"Innalillahi wa'inna alaihi raji'un"_ abinda Nawaz keta faman furtawa kenan. A hankali taji wannan nauyin da mararta tayi ya koma yana mata waiwayi me ƙarfin gaske kuma yana shirin zubowa ta ƙasanta _"ka matsa kada na ɓata maka jiki, fitsarin zai zubo"_ Jin Abinda tace yasa Aayaan ya Maida bakinshi saitin gurin da sauri don bazai yarda yayi missing ɗin wannan love milk ɗin ba, adaidai lokacin kuma Nawaz ta kama kanshi da ƙarfi jikinta na wani irin rawa kamar mazari tare da sakin wata yar ƙara "yaya zan mutuuuu" A cikin bakinshi duka cums ɗin ya zuba inda a cikin zuciyarshi yace _"it's time for the next page"_ Sosai jikin Nawaz ya saki inda ko motsi ƙwaƙwƙwara bata iyayin, gaba ɗaya ta rasa meke mata daɗi, ita batasan abin har yakai haka ba! Da ita a zatonta tsoma jelarshi Aayaan zaiyi a HQ ɗin ta kawai, idan yayi releasing ya cire ya ƙara gaba, to Ashe aikin Babba ne. Sosai ya koma samanta tare dayi mata rumfa yana haɗe bakinsu guri ɗaya inda kuma yake bin duka sassan jikinta softly yana shafata da hannunshi na dama. Jinda tayi yana karanto addu'ar saduwa da iyali ga kuma taji alamun zai tura mata Abin datasan muddin ta bari ya tura to saidai wata Nawaz ɗin amma ba ita ba, danno kirjinta tayi sama da nufin son kwace kanta. Aikuwa take Aayaan ya sakin mata nauyi tare da danna ta ƙasa domin a wannan lokacin *No going back* taken nasu na sojoji. Sakin ƙara Nawaz tayi jin wani irin kakkaura kuma sandararren Abu me dumi yana ratsawa ta cikin jikinta, Saboda girmanshi saida Aayaan ɗin yasa karfi yana dannawa sannan ya fara shiga, wata irin azaba taji tana ratsata me ɗaukar hankali, Dukanshi ta farayi tako ina tana cewa "wallahi baka sona, ka kyale Ni, wayyooo mummy! Ummina kizo ki ceceni!!!! "Aunty Aseey kizo Aayaan zai kasheni, na shiga Uku, Wallahi saika sakeni, kuma saika maidani gida. Shikam Aayann a lokacin koda kasheshi zatayi sai dai ta kashe shi domin bai san ma a wace Nahiyar yake ba, ya shiga wata irin duniya me wuyar kwatanta wa, burinshi kawai yajishi a G-spot ɗinta, hakan nema yasa ya sa duka hannuwanshi ya ɗago bum-bum ɗinta yayo sama da ƙugunta Yadda Zai shiga can ciki, sosai ya Maida himma a penetrating, yana sauke wasu irin numfashi masu ɗumi da sauri da sauri inda kuma daga bisani ya fara maganganun da nima bazan iya faɗa ba 🙈🙈, Wanda na faɗa ma sun isa. Yadda ya dage yana entrusting a saman marar Nawaz shi zai tabbatar maka cewa baya cikin hankalinshi, Domin da yana cikin hayyacinshi bazai dage yana wannan aika aikar ba, tunda da bakinshi yayi mata Alƙawarin to be more gentle on her. Nawaz taga Duniya! don gaba ɗaya cire raima tayi da rayuwar Duniya, tun tana ganin zai dena har Saida gaba ɗaya jikinta ya mutu numfashinta ya ɗauke gaba ɗaya. A lokacin da shi kuma Aayaan yaji Kamar an tattaro duka wani nauyi da wahalar duniya ne sunyo waje gaba ɗaya, Abinda ko a mafarki be taɓa tunanin zai taɓa jin irinshiba yake ji tare dashi, take jikinshi ya ɗauki rawa saboda irin yadda sperm ɗin ya tawo me uban yawan gaske kuma in a high speed, kuka ne ya kucfe mishi be shirya ba sannan yanajin kamar Zai sume, kama Nawaz yayi ya kamƙameta kamar ance za'a rabashi da ita har abada, Wata irin gamsuwa ce ta kama shi mai cike da nutsuwa. A hankali yake maida numfashi amma idonshi a rufe yake, wani irin abu ne yaji yana ratsa duka jijiya da tsokar jikinshi, "Lallai dole Nawaz ta riƙa yi mishi kwalele, haka abin yake dama? Maida nunfashi yaci gaba dayi a hankali tare dayin tunanin me zaiyi wa Nawaz a Matsayin kyautar wannan sabuwar diniyar data sakashi? "Sweetheart ki faɗi kome kikeso i promise zanyi" Shiru yaji bejin koda Alamun numfashinta, da sauri ya buɗe ido yana duba pulse rate ɗinta cikin tashin hankali, ahankali yaji yana bugawa Alamun ta daɗe da suma. Bakinshi ya haɗe da nata yana bata mouth To mouth breathing, wani irin Gwauron numfashi Nawaz ta sauke tare da wasu hawaye masu ɗumi da suka zubo ta gefen idanuwanta. "I'm very sorry dear, wallahi kedin ce saiki kashe mutum, wannan gumurzu haka!" Wani irin takaici ne ya kama Nawaz "wato itace ma zata kasheshi bashine Zai kashe taba! Duk wannan Uwar azabar daya gana mata har yanada bakin iya yi mata Magana. Fashewa tayi da kuka sannan cikin dashasshiyar murya wadda daƙyar take fita tace "Wallahi ka maidani gidanmu tunda kai mugu ne! Jifa yadda ka gana min azaba ka wahalar dani amma kanada bakin cewa zan kashe ka, to waye a cikinmu yayi niyyar kashe wani? "Sweetheart rigima, pls banaso kina magana domin kina wahalar min da kanki, ba wai da wahala nake nufi zaki kasheni ba da ɗayan nake nufi 😉, nasan ai kin gane me nake nufi." Fashewa ta karayi da kuka tana cewa "Wallahi kai mugune kuma Mun bata Daga yau, babu ruwana dakai tunda bakada imani, And kuma ka sani cewa dole nema ka maidani gida Idan gari ya waye" Sosai yake jin tausayinta domin tabbas yasan ya wahalar da ita matuka, be taɓa tunanin zai fita daga hayyacinshi irin haka ba, ta shayar dashi, wata irin zuma me garɗi da zaƙi, Ni'ima, gamsuwa da sukunin da be taɓa tunanin akwaishi a duniya ba. Don haka ta taka wani tsanin da babu wata ƴa mace da yake tunanin zata taɓa taka shi. Wani matsayi na musamman yabata a Cikin zuciyarshi, domin Dalilin ta ya fara fitar da cinkushashshen dafin daya cunkushe mishi a mara, a yanzu haka jinshi yakeyi Kamar sabon mutun, sakayau kuma babu wani Abu da yake damunshi a faɗin duniyar nan. Wata irin ƙaunarta ce ke yawo a duka sassan jikinshi, yanajin zai iya yin komai akanta sannan zai iya ɓata wa da kowa dalilin ta. Samun kanshi yayi d5 ƙara rungumeta a cikin jikinshi yana cewa "Allah yayi miki Albarka, Allah yasa ki gama da Duniya lafiya, Allah ya Al-barkaci rayuwarki, ina ƙaunarki Madina Al-munawwarah, ki faɗi kome kikeso a cikin faɗin duniyar nan, Ni kuma i am ready to offer it" Cikin muryarta wadda take nuna irin wahalar datasha tace "ka maidani gida" Wani irin ɗaci yaji ƙirjinshi yayi mishi, ko a da dabai san Ni'imar dake tattare da ita ba ai bazai iya maida ita gida ba, balle Yanzu data shayar dashi irin Tata zumar. "Pls sweetheart kada ki kuma cewa in maida ke gida saboda ji nakeyi kamar zuciya ta zata fashe, Wallahi bazan iya Rayuwa babu ke a tare dani ba, ki zaɓi wani abu pls Amma banda nisantani dake" Shiru kawai Nawaz tayi tana sauraron zugin da jikinta yakeyi, gaba ɗaya ko ina zafi yakeyi mata, musamman HQ ɗin ta da takeji kamar zai zazzago ya faɗo. A hankali Aayaan yaji zazzaɓi ya fara rufeshi, ganin da gaske zazzaɓin ne zai kama shi yasa yayi himmar tashi don gyara Nawaz. Wani irin sanyi yakeji yana shigarshi ta duka tsigar jikinshi, koda yamiƙe sai ya ƙarasa ya kunna bulbs ɗin, haskene ya gauraye duka Dakin, towel ɗin daya ɗaura sanda yayi wanka ya ɗauka ya kuma ɗaurawa, ita kuma nawaz dama idonta a rufe yake sannan rufe take da duvet, komawa yayi kusa da ita tare da yaye duvet ɗin yana ƙoƙarin buɗe tsakanin cinyoyinta data haɗe su guri ɗaya, so yake yi ya duba ko yaji mata ciwo, ƙanƙame jikinta tayi tana jin wani sabon tsoro yana shigarta *To ƴan gulma yau dai an kashe boss* *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *75* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Sweetheart pls ki barni zan duba jikinki ne, babu Abinda zanyi miki. Ɗan sakin jikinta tayi amma still Idonta a rufe gam, tanajinshi ya buɗe cinyoyin ya duba "Alhamdulillah!!! Allah na gode maka, gaskiya Allah yanasona da yawa" Ɗagota yayi yana cewa "sweetheart bakiji ciwo ba, dama inata tunanin ta yadda zan yi miki stitching saboda tausayinki nakeji, ace duk wannan wahalar da kikasha bazata tsaya iya nan ba, gashi kuma bazan iya barin kowa ya ganin mini guri mai matuƙar muhimmanci a rayuwata ba. Duk Abinda yake faɗa jinshi takeyi kamar yana yi mata tatsuniya ne, ya za ayi ma Yace mata bataji ciwo ba? Duk wannan Uwar azaba da zugin da takeji a cikin jikinta ta ina suke zuwa? Zuwa wannan lokacin zazzaɓin ya riga yaci ƙarfin shi amma jarumta ta hana ya nuna, don wani irin sanyi ne yake ratsashi tako ina ga jiri Jiri da yake gani, ajiyeta yayi Sannan ya shiga bayin ya haɗa ruwan zafin ɗan dai-dai Yadda bazai chutar da itaba, farincikin shi ɗaya ma da bataji ciwo ba. Komawa yayi ya ɗauko ta ya nufi Cikin bayin da ita, cikin dabara ya sakata cikin ruwan zafin, ai kuwa take ta saki wata Uwar ƙara, babu shiri Aayaann ya cireta daga cikin ruwan yana cewa i am sorry dear, taɓa ruwan yayi don tabbatar da yanayin zafin shi, NORMAL yaji shi amma yasan ita dole taji zafinshi saboda ciwon dake jikinta. Ƙara sirka ruwan yayi sannan ya ɗauke ta chak a kirjin shi, shiga cikin ruwan yayi rungume da ita, har zata fara wani ihun taganshi acikin ruwan shida ba ciwo gareshi ba, hakanan ta daure duk da Irin azabar dake ratsata, gaba ɗaya gashin kanta da goshinta sun jiƙe da gumi, sosai tausayinta ya kamashi domin yasan dole taji zafi kuma shine silar komai. Saida ya chanza mata Ruwan so uku sannan yayi mata wankan tsarki tare dana sabulu, goyata yayi a bayanshi sannan ya fita zuwa bedroom ɗin, yaye zanin gadon yayi ya ajiye a gefe sannan ya ƙarasa ya buɗe wardrobe ya ciro wani bedsheet ɗin yayi spreading dinshi. Kwantar da Nawaz yayi ya gyara mata kwanciya Sannan ya janyo duvet ya rufeta dashi, bayin ya koma inda shima yayi nashi wankan, koda ya fito Lokacin Nawaz ta riga tayi barci, kissing ɗinta yayi a goshi tare da cewa "I Love You sweetheart! You mean everything to me" sannan ya ɗauki jallabiyarshi yasa tare da matsawa saman carpet ya tada kabbara. Sallah yayi tayi raka'a bibbiyu har saida yaji jiri na neman kada shi ƙasa sannan ya haƙura ya zauna ya fara zuba addu'oi, sosai yayiwa Allah kirari tare da gode mishi bisa baiwar da yayi mishi na bashi Nawaz a Matsayin mata, kuma dukda Kasancewar ta daɗe batayi Aure ba ya sameta a cikakkiyar budurwa Abinda yayi ƙaranci a zamanin yanzu kenan, addu'oi yayi musu sosai akan Allah ya basu zaman Lafiya ya albarkacesu da ƴaƴa na gari. zuwa lokacin zazzaɓin yaci ƙarfin shi, kasa tashi yayi Daga inda yake, Sai kawai ya koma ya kwanta a Saman carpet ɗin Tare da curewa waje ɗaya saboda sanyin da yakeji yana Ratsa duka sassan jikinshi zuwa ɓargonshi. Kafin wani lokaci jikinshi yayi wani irin zafi rau, haƙoranshi har haɗewa da juna sukeyi, sanyi sosai yakeji amma ya kasa tashi ya ɗauki bargo ya rufa. Itakam Nawaz tanata barcinta wanda bata samu tayi da dare ba, sai bayan kamar awa biyu wani irin fitsari ya tasheta daga barcin da takeyi, koda ta tashi zaune bataga Aayaan kusa da ita ba, Hannu tasa ta janyo towel ɗin daya zame daga jikinta sanda tana barci ta ɗaura Sannan a hankali ta miƙe tsaye, takawa ta farayi a hankali Amma tana ɗan jin zugi a HQ ɗin ta, a haka ta daddafa ta shiga bathroom ɗin tayi fitsarin ta fito, ga mamakin ta ganin Aayaan tayi a ƙudundune saman carpet yana rawar sanyi, sannan tanajin gunjin numfashinshi irin wanda zazzaɓi yayiwa mugun kamu. Neman zafin da takeji tayi ta rasa, ita kanta Batasan sanda ta isa gareshi ba Tare da ɗago kanshi tana cewa "yaya meya sameka? Rau haka taji jikinshi kamar garwashin wuta, rasa yadda zatayi tayi sai kawai ta fashe da kuka tare da cewa "nashiga uku! Don Allah meya sameka? Ganin bazai bata amsaba yasa ta samu gefen shi ta kwanta inda ta shige cikin ƙirjinshi ta rungumeshi gaba ɗaya, cigaba da kukan tayi Saboda bata sanma me zatayi ba. Hankalin Aayaan yayi mugun tashi sanda yaji maganar Nawaz a kusa dashi saboda yasan ba wani iya takawa zatayi ba dakyau, ya kamata ace shi zaiyi jinyarta bawai ita tayi tashi ba, yanaso yayi mata magana Amma ya kasa saboda yadda bakinshi yayi mishi Nauyi, daurewa yayi ya buɗe bakin a hankali Tare Da cewa "Dear bakida Lafiya shine kika tashi" NAWAZ taji alamun yana magana Amma bataji me yace ba saboda Yadda muryarshi tayi ƙasa, "yaya I'm sorry pls, ka taimakeni ka tashi daga kasan nan ka hau Saman gado... Ganin cewa ko yayi maganar baji takeyiba yasa ya fara girgiza mata kai Alamun ta gane ba zai iya ba. "Bazaka iya ba?" "Ɗaga mata kai yayi Alamun "eh", sosai tausayinshi ya kamata, gaba ɗaya ma neman haushinshi da takeji tayi ta rasa. Yanzu burinta be wuce taganshi ya tashi ba, ace ingarman mutum Irin wannan ne kwance yana rawar zazzaɓi? Lallai koma menene ke damunshi ya Isa Abin dubawa. Ahaka tana tunani barci yayi awon gaba da ita, sai Misalin ƙarfe shida da wani Abu ta tashi, shima tana cikin barci taji Kamar Ana kissing ɗinta, a hankali ta buɗe idonta wanda yake cike da barci, fess ta saukesu a saman fuskar Aayaan wanda yake yi mata wani kyakkyawan murmushi. "Dear tashi kiyi sallah mun makara" Maida idonta tayi ta rufe Saboda tuna Abinda ya faru Tsakanin su jiya da dare da tayi, da sauri kuma ta kuma buɗe idon tare da cewa "mafarki nayi ko gaske?" "Kinganni banida Lafiya Koh? To gaskene! Da gaske nayi zazzaɓi na wucin Gadi" Amma Yanzu naji sauƙi Maida Idonta tayi ta rufe tare da cewa "Allah ya ƙara sauƙi amma Naji tsoro sosai wallahi" A hankali kanta a ƙasa ta tashi tare dasa ƙafarta a saman carpet da niyyar sauka daga kan gadon, ai kam bata Ankara ba taji Aayaan yayi sama da Ita tare da cewa "Ayyah Madam ɗina nasona Ashe?, muje Kiyi alwalar to" Sai a cikin bathroom ɗin ya Sauketa tare da kunna mata tap ɗin sink "kiyi alwalar sai in maidake kiyi sallar" "Nifa zan iya tafiya da kaina! Ka tafi kawai" Nawaz tace domin ta kasa sakewa sam "Just keep quiet and do what you Are here for" Shiru tayi tai alwalar, fara takawa tayi da kanta saboda ita sam ba wani ciwo takeji na azo agani ba, "ɗage ta sama yayi tare da cewa "meyasa kikeson tsokana tane?, Uhhm?" Ita kunyarshi takeji amma shi ba zai gane ba, sai yayi ta ƙara sa tanajin kunyar. A saman carpet ya ajiyeta ya sa mata doguwar rigarta sannan ya yane mata kanta da mayafi Sannan yace "to Bismillah" Tada iƙama tayi shikuma ya tafi kitchen don ya haɗa mata tea me zafi saboda ta gasa mararta, bashida magani wanda ya danganci condition ɗin da Nawaz take ciki a cikin first aid box Dinshi, kuma Abin yazo mishi a bazata shiyasa be shirya komai ba. Sanda ya kawo mata clove tea ɗin ya Tarar harta idar da Sallah, ɗaukarta yayi ya ɗora ta a saman cinyarshi tare da kafa mata kofin a bakinta "Bismillah" A hankali ta fara sipping ɗin tea n, sosai yayi mata daɗi Saboda yasa zuma da yawa a ciki, saida ta kusa shanyewa tace ya isheta, murmushi yayi ya shanye sauran tare da ajiye cup ɗin a saman side drawer. Ɗaukarta yayi ya ɗora saman gadon tare da rungumeta a Cikin ƙirjinshi "Sleep" Abinda yace mata kenan ya shiga duniyar tunani "me zanyiwa Nawaz a duniyar nan na biyata? What will suite her? " Sosai yake Duba meya dace da Ita, komai ya kissifa a ranshi sai yaga beyi mishi ba, yayi kaɗan ko kuma darajar ta tafi Abin. A haka shima barci ya dauke shi dama ita Tun tuni tayi nata barcin. Bashi ya tashiba sai wajejen ƙarfe Goma, koda ya tashi ita bata tashiba sai barcinta takeyi hankali kwance, a hankali ya gyara mata kwanciya Tare Da ƙara rufeta da duvet. Tashi yayi saboda yaje CLINIC ya siyo mata magunguna duk da ya lura jikin nata Alhamdullillah, zazzaɓi ne kawai yake damunta sai kuma zargin da yakeyi akan ta saboda zazzaɓin da yayi. Yana tunanin idan Hakan ta kasance shikam ya zaiyi da farin ciki? Yana buɗe kofa sukayi ido huɗu da fatima zata danna ƙararrawa, gaisheshi suka fara yi a ɗan daburce ita da Maman sudeis dake tsaye bayanta, murmushi yayi musu Sannan ya amsa tare dace musu "sannunku da zuwa, ina abokina?" "Aikam gashi yana barci, dama yau munyi zamuzo mata yini ne, to kuma mun kira wayarka amma ba'a picking shine mukace bari mu tawo kawai" maman sudeis tace tana ɗan murmushi. "Ayyah wayar na ɗayan bedroom ɗinne, dayake ba'a nan muka kwana ba, kushiga tana ciki tana barci ne. Nuna musu ɗakin da take ciki yayi Sannan ya fita ya barsu a falour, maman sudeis ce tace "Anya kuwa Fatima ba'a kashe boss ba? Naga yanata murmushi, kuma wane barci ne har shadaya saura? "Uuhmm nidai Babu ruwana, kinganki dasa ido, kin tasa Yar mutane a gaba" Miƙewa Maman sudeis tayi ta shiga bedroom ɗin da Aayaan yace Nawaz na ciki, Yadda taga Komai a yamutse yasa ta yafito Fatima da hannu Alamun tazo. Bin bayanta Fatima tayi itama ta shiga ɗakin, bin ɗakin suke da kallo Domin suma ya tafi da imaninsu, zanin gadon da Aayaan ya ajiye a gefe sanda ya chanza ɗayan Maman sudeis ta ɗauka tana kallo, ƙwalalo Ido tayi tare da cewa Fatima dama nace Miki........... Babu yawa Amin afuwa. *MATAR RASHEED* ✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *76* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* "Fatima dama nace Miki an kashe boss, kalli kiga" Cewar maman sudeis tana nunawa fatima stain ɗin dake jikin zanin gadon "Ni dai ajiye mu fita kada ta tashi ta gammu kisa muji kunya" Cewar Fatima tana yin hanyar fita daga faloun. Shara da kakkaɓe-kakkaɓen ƙura sukayi mata da ƴan gyare-gyare amma iya falour da kitchen sai ɗaya bedroom ɗinsu wanda suke kwana da. Maman sudeis ce tace "Anya kuwa fatima bazamu dafa musu wani Abu ba! Nasan ba wani abu suka ci ba kuma Dole bakinta babu daɗi" "Eh ya kamata amma kamar me" "Mu fara duba freezer muga abubuwan dake ciki, Kinga sai musan me ya dace a girka" "To" Fatima tace tare da miƙewa Sannan suka nufi kitchen Dukansu..... Bubu abinda babu a cikin freezer ɗin, nadaga kaji, kifi dasu vegetables. Kaji biyu Maman sudeis ta ciro da kayan lambu sai catfish guda uku manya, kifin taba fatima tace ta gyara ita kuma ta daɗa ɗauraye kazar ta ɗora a wuta tare dayi mata haɗin tafashe. Sosai aikinsu yayi nisa inda har sun gama pepper chicken da roast fish, fried rice ɗinne basu gama ba, babu Nawaz babu alamunta, hakan ke nuna har yanzu bata tashi ba, shima kuma Aayaan har yanzu be dawo ba. A ɗaki kuma tashin Nawaz kenan daga barci taga babu Aayaan, sosai taji daɗi Saboda zatayi komai a sake tunda shi ya kase gane tana jin kunyar shi, miƙewa tayi a hankali ta fara tafiya, ita kanta mamakin ya akayi batajin irin mugun zafin nan takeyi, tasan dai tanajin zugi amma ba Irin wanda take tunani ba "kenan Sarfraz mugunta yayiwa hassu, tunda har fa ɗinki akayi mata" bathroom ɗin ta shiga a hankali tare da kunna tap ɗin water heater. Bath ta cika da Ruwan zafi Sannan ta sirka zuwa yadda zata iya shiga, cire rigar jikinta tayi sannan ta shiga cikin Ruwan a hankali, daɗi sosai Ruwan yayi Mata, tayi kwance luf a ciki dumin na ratsa ta tako ina. Saida ta canza ruwan har sau uku Sannan ta haƙura tayi wanka ta fito, zanin gadon dake gefe ta ɗauka ta koma bayin ta tura shi cikin washing machine ta zuba ruwa da liquid soap. Bedroom ɗin ta dawo ta samu mai a cikin drawer ta mutstsika a jikinta sannan ta feshe duka jikinta da turare, rasa kayan da zata sa tayi saboda babu kaya a cikin wardrobe ɗin. Tana tunanin fita zuwa ɗauko kayan saboda kada su haɗu da Aayaan kila yana falour ko kitchen, gashi kuma towel ne Kawai a jikinta, shiru tayi naɗan wani lokaci inda daga bisani ta koma bathroom ɗin ta ɗauko doguwar rigarta ta mayar jikinta tunda dama Sallah kawai tayi da ita bawai tayi datti bane. Tufke gashin kanta tayi daya dameta a fuska Sannan tayi hanyar fita falour saboda cikinta ya fara kiran ciroma, mamaki abin yaba Nawaz ganin maman sudeis da Fatima hakimce a kujera sunata shan hira "lah! Ikon Allah! Don Allah yaushe kuka zo gidan nan? Ina yayan yake?" "Hmmm Madina kenan, nifa har yanzu na kasa yarda ba ciki gareki ba, wannan uban barci kamar barcin mutuwa" Cewar maman sudeis tana kannewa fatima ido Ita kuma Fatima tace "Tun ƙarfe goma muna nan gidan fa, yayan naki kuma ya fita tun sanda mukazo" "Kai dan Allah! Shine ko ku tasheni!" "Hmmm Madina manya, mu munsan meya saki Barci ne da zamu tashe ki?, muje mu tasheki mu samu zunubi" "Kai Don Allah wane zunubi kuma" Nawaz tace tana yin hanyar kitchen, sosai ta gyara rafiyarta saboda kada su fuskanci wani abu (Nikam nace hajiya Madina kin makaro, ai duk wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi, balle kuma sun gani da idonsu) "Bari ko noodles na dafa muku, kuna zaune tun tuni da yunwa" "Mun hutasshe ki, aimu nan budirinmu mukayi a kitchen ɗin" fatima tace tana tashi don bin bayan Nawaz ɗin, buɗe mata komai tayi. Mamaki sosai ya kama Nawaz, kuma sosai taji daɗi Don dama wata Irin baƙar yunwa ke sakaɗar ta, godiya tayi ta musu Sannan ta zuba, tumbler ta ɗauka ta zuba juice ɗin gwandar da Fatima tayi "wai kunma ci kuwa" "A'a! Ya za'a yi muci fisbilillah? Daga gama dafa abinci sai mu diba muhau ci?" "Au to kada kuci, har kuka iya girkawa, wato ci ne bazaku iyaba, to ku jira in zuba muku!" Fita tayi daga kitchen ɗin tana ɗan yamutsa fuska saboda mararta data ɗan ƙulle mata, a kujera ta zauna ta fara ci a hankali, sosai taji daɗin girkin barin dama ga yunwa ga jiki Babu daɗi. Suma dai zubowa sukayi sunaci suna jefa hira kaɗan kaɗan, ita dai Nawaz da ido ta bisu tana mamakin ina Aayaan yaje da har Yanzu be dawo ba? Bata gama tunanin ba saiga ƙarar turo ƙofa, Aayaan ne ya shigo da Sallama, yama manta da su maman sudeis sunzo, nufar Nawaz yayi da sauri, duƙawa yayi ya sumbaci goshinta Sannan ya rungumeta "im sorry dear, nabarki ke kaɗai ko? Kin kuma shiga cikin Ruwan zafin kuwa" Toshe mishi baki tayi da sauri tare da cewa "su maman sudeis a bayanka fa" a hankaki yadda bazasu jita ba Ware idonshi yayi, don gaba ɗaya ya manta cewa sunzo, waigawa yayi sai yaga basu suke kallo ba "Sannunku maman sudeis" ""Yauwa sannu an dawo lafiya" suka ce ita da Fatima "Lafiya Lau Alhamdullillah, abikina be tashi ba" "Ya tashi komawa yayi" "Allah Sarki ai gara ya huta" Cewar Aayaan wanda yake yiwa Nawaz sign da ido na su shiga cikin daki, ita kuma sai ta nuna bata gane me yake nufi ba domin tana jin kunyar ta bishi su maman sudeis na zaune Tashi yayi ya shiga cikin Don be so ya takurata tunda ya lura batason zuwa, ci gaba da cin abincinta tayi bata ko kalli inda yabi ba Maman sudeis ce tace "wai kam Madina don Allah shekararki nawa ne?" Cikin rashin damuwa Nawaz tace "ishirin da biyar" Kallonta maman sudeis tayi tace "kodai sha biyar?" "Kai maman sudeis, sha biyar kuma! Allah ishirin da biyar ne harda ƴan watanni" "To lallai kam Abin naki harda iskanci, inba raini ba mijinki ya dawo babu tarba, babu sannu da zuwa, Sannan ya shiga ɗaki kin yi banza dashi, Anya kuwa madina🤔🤔 to wallahi maza ki tashi kije kitchen zakiga wanda na zuba mishi a madaidaiciyar warmer sai juice ɗinshi a jug, kiyi maza ki kai mishi, wallahi madina ko jinnul ashiq gareki saiya barki hardai ina tare dake, idan kuma so kike ya fara sha'awar ƙara Aure to." Gaban Nawaz ne ya faɗi rass jin maganar maman sudeis ta ƙarshe, tashi tayi ta nufi kitchen ɗin don ɗauko abincin Kamar Yadda maman sudeis tace mata. Fatima ce ta kyalkyale da dariya " maman sudeis wollah bakida dama, ji yadda kika zage kinayiwa ƴar mutane faɗa Kamar ƴar ki?" "Ai Madinar ce sai da wuta, sam Batasan Irin damar da Allah ya bata bane, ji shekarunta amma sam babu wayau, ai inanan saina saita ta a layi tukuna" "Ai kam kina samun lada Wallahi, tunda jiya sanadin ki an kashe basawa! Don sunfi ƙarfin boss" Banza da ita maman sudeis tayi tana harararta irin na wasa. Warmer da jug ɗin Nawaz ta zuba a saman tray tare da tumbler da cokali ta ɗauko na nufi hanyar bedroom ɗin ko kallon su maman sudeis batayiba wai irin ita tayi fushin nan, aikam tana shiga suma suka kwashe da dariya "Anaso ana kaiwa kasuwa" A zaune ta Tarar dashi saman stool, yana ganin ita ce yayi saurin miƙewa tare da Amsar tray ɗin daga hannunta yana ɗaurawa saman mini table ɗin dake gabanshi "sweetheart bakida lafiya fa! Meyasa zaki wahalar da kanki haka, aida kin kirani na ɗaukar miki, zo ki zauna Anan. Janyota yayi ya ɗorata a saman cinyarshi, a hankali Nawaz tace "Ina kwana yaya" "Lafiya Lau Madam, kintashi lafiya? Ya ƙarfin jiki? Jiya nayi gagarumin laifi Koh? Duƙar dakai Nawaz tayi, don itafa bataso yana yin Irin wadannan maganganun, ji take kamar ta ruga da gudu. "Baza'a bani amsa ba?" Aayaan yace yana jan karan hancinta kaɗan. "Ina kaje ne? Na tashi baka nan" Nawaz tace don ta kauda maganar da yakeyi mata "Sirri ne! Amma idan za'a min kyauta zan faɗa " Aayaan yace yana kanne ido ɗaya, sai kuma ya ɗage girarshi sama. Still dai Kanta a duke tace "me nake dashi dazan baka?" Da sauri ya rufe mata baki tare da cewa "ai kin gama bani komai jiya, duk Abinda zan yi miki bazan iya biyan kiba, sai dai inyi mana fatan ko a aljanna mu kasance tare. "Kaci abincin please, nasan ba Lallai kaci wani abuba" yanzu ma tace hakan ne saboda abar maganar. Sosai Aayaann yaji daɗin Yadda ta nuna ta damu dashi, buɗe warmer ɗin yayi yasa cokali ya debo abincin ya nufi bakin Nawaz dashi, amsa tayi saboda kada ta Gwale shi sai kuma tace "yaya Ni na koshi, wannan nakane" "Okay to Nagode, May Almighty Allah bless you with well mannered children " Ɗan murmushi Nawaz tayi tana tunanin yaushe akayi daren da har gari zai waye. Sosai yaci abincin Sannan ya ɗauki jug ɗin yasha juice ɗin, shima sosai yasha saboda natural ne kuma sosai yayi mishi daɗi. "Madam zanyi wanka! Ko zaki min?" Da sauri Nawaz ta tashi daga jikinshi tayi hanyar kofa da sauri Tare Da cewa "idan ka gama ka shirya zan dawo "murmushi yayi ya juya ya shige bathroom ɗin. Ita kuma Nawaz ta fice zuwa falour, a tsaye ta tarar dasu maman sudeis da Fatima, Alamun sun shirya zasu tafi gida "kada kuce min zaku tafi ne?" "Wallahi tafiya zamuyi munyi da oga zai dawo wurin ƙarfe huɗu, kuma babu Abinda nayi a gida" "Okay to ku bari ya fito daga wanka sai ya samar muku cab ta maida ku" Nawaz tace tana murmushi "Wai me kika maida mu ne Madinah? Komai kice sai anyi mana, to mudai kinga tafiyarmu, ki barshi ya huta, yanzu fa ya dawo" ficewa sukayi daga Ɗakin tare da Turo mata kofar suka rufe. Nawaz na tsaye tana mamakin su maman sudeis kusan minti uku, sai kuma ta kaɗa kai tayi hanyar bedroom ɗinsu wanda suke kwana a ciki da, shima tsaff su maman sudeis sun gyara shi, samun kanta tayi da kwanciya tayi dai dai. Takai minti Kusan goma sha biyar a keance sai kuma ta tashi zaune da sauri Tare da cewa "innalillahi wa'inna alaihi raji'un, yai sam bansha maganina ba gashi nayi alkawarin kullum saina sha. Tashi tayi ta nufi kitchen ɗin, tana shiga ta buɗe drawer data ɓoye maganin ta ciroshi, ji kawai tayi Aayaann ya rungumeta ta baya tare da cewa "Sweetheart me kikeyi a kitchen, kuma fa kinyi alkawarin zaki dawo gurina" Murmushin tayi saboda ta kasa cewa komai, ita damuwarta bata wuce maganin dake hannunta a fili ba, kada yace ta bashi saboda maman sudeis tace kada ta bari ya gani. Amsar maganin yayi ba tare daya yi mata magana ba, bayanta gama karanta label Dinshi sai yayi murmushi "dear meya haɗaki da blood cleanser kuma? "Maman sudeis ce ta bani sanda banida lafiya tace na riƙa shan biyu safe biyu rana biyu dare. "Ashe likita ce itama" Aayaann yace yana ƙoƙarin buɗe murfin robar "A'a kawai dai tace wai tayi Amfani dashine taji daɗin shi" Zaro ido Aayaan yayi bayan ya buɗe murfin robar ganin kwayoyin da suke ciki, idan idonshi beyi mishi karya ba highly effective aphrodisiac pills ya gani a ciki, zazzago su yayi don ya ƙara tabbatar wa. Ile kuwa sune, mamaki sosai ya kama shi amma be bari Nawaz ɗin ta lura ba, "yaushe ta baki" "Sanda mukaje gidanta" Cewar Nawaz tana ɗan yin mutsu mutsu Alamun ta gaji da tsayuwar Murmushine ya kwacewa Aayaan, kenan duk uban ciwon nan da Nawaz tayi feelings ke damunta amma taƙi ta faɗa mishi, lallai kunyarta har tayi yawa, kuma mamakin shi ɗaya shine ya akayi maman sudeis ta gane wani Abu be taɓa shiga tsakaninsu ba da har tayi irin wannan dabarar? "Lallai kam Dole zanje inga Maman sudeis gani na musamman, kuma inaso ta faɗa min a ina tasan maganin nan, domin ni kaina ba ƙaramin taimakona yayi ba. Ɗaukarta yayi chak tare da cewa "muje kiji Wata magana! Saura kuma ki min raki Kuyi haƙuri da typing errors banyi Editing ba🥱 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *77* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Jin hakan daya ce take jikin Nawaz ya fara rawa, kada fa yace wani Abu zai kuma yi mata. Murmushi Aayaan yayi "Meye kuma na rawar jiki, why are you so lazy? Kefa matar soja ce! Yakamata ki zama jaruma tako wane fanni, just yadda ake harba bindiga fa zan koya miki ba wani abuba. "Nima fa bance wani abu ba" "To ai jikinki yace" Cewar Aayaan yana kanne mata Ido. Bathroom ya zarce da ita inda ya kuma gasa mata jikinta Sannan yayi mata wanka, tana gefe shima ya fara nashi wankan. Ita dai rufe ido tayi har ya gama ya ɗaura towel sannan ya daukota ya fito harabar bedroom ɗin, dayake bedroom ɗin da kayansu yake ciki suka shiga, buɗe wardrobe yayi ya zaɓo mata doguwar riga me kyau da Babban mayafi, shima wardrobe Dinshi ya buɗe ya ɗauki farar polo shirt me gajeren hannu da black jeans, Tsaff suka shirya gwanin sha'awa, kowa ya gansu sai sun birgeshi, "zamuje Hampton garden achan zan koya miki yadda ake operating ɗin bindiga da komai nata, kuma saura kimini raki!, Inaga daga chan ma mu biya Asibiti gurin haidar" "Toshikenan in'sha Allah bazan baka kunya ba..." "Subhanallah! Na manta da magungunan dana siyo Miki a Mota, sai kuma Babbar kyautar ki ta shayar dani Ni'imtacciyar madara natsuwa da kikayi." Duƙar da kai Nawaz tayi "Nidai don Allah ka dena bani kunya" "Wai wannan kunyar yaushe zata barni na huta ne?" Cewar Aayaan yana ɗaukarta Fita sukayi daga ɗakin inda ya rufe kofar suka shiga cikin lifter, be sauke taba har saida ya saka ta a cikin mota sannan shima ya zagaya ya shiga gefen driver. Drawer ɗin cikin motar ya buɗe ya ciro wata polythene bag madaidaiciya, wani madaidaicin akwati ya ciro a cikin jakar ya buɗe, wata Irin sarƙa ce a ciki sai walwali takeyi Saboda fararen duwatsun da aka ƙawata ta dashi, haɗe take da Abin hannun da ɗan kunne sai zobe. Kusa da ita ya matsa sosai sannan ya zame mayafin kanta, sarkar ya fara sa mata sannan ɗan kunnen sai Abin hannu da zoben. Sosai sarkar ta birge Nawaz sai kallon zoben takeyi tana murmushi, yana gama sa mata tace "Nagode sosai, Allah ya saka da Alkhairi ya ƙara budi ya rufa asiri, ya tsare kullum sannan yasa kafi haka" Toshe mata baki Aayaan yayi tare da cewa "ke kika fara min kyauta shiyasa nima nayi Miki, kinga kenan ba gode min zakiyi ba, and kuma tun tuni nace miki komai nawa nakine! No need ki riƙa min godiya" Amma sosai yaji daɗin addu'ar datayi mishi har cikin zuciyarshi... "Hmm yaya kenan! Ai ko ajiya na baka idan na amsa dole na gode maka, balle bansan dashiba ka bani" Magungunan ya cirar mata sannan a ɗauki ruwa a beverage pack ɗin dake cikin motar ya buɗe mata, a baki ya kafa mata ruwan Sannan ya cire ya zuba mata maganin ya kuma maida mata da ruwan bakinta. Saida ya tabbatar tasha ruwan da yawa yadda maganin zai fara aiki da wuri Sannan ya ajiye robar ya maida hankalinshi gurin kunna motar, tuƙi yakeyi a hankali dayya hannunshi yana rike dana Nawaz wanda ke gefenshi. Ita dai tana zaune ne kamar gunki, takarda ta gani a cikin ledar da Aayaan ya ciro dan akwatin sarkar daya sa mata, ɗaya hannun da Aayaan be riƙe ba tasa ta ciro takardar tana dubawa. Receipt ne na sarkar daya siyan mata, kallon takardar Nawaz take tana kallon Aayaan, duk hankalinta ya tashi ta zaro ido waje "yaya naga ansa 2.5million a jikin receipt ɗin nan" "Menene" "Wai kana nufin haka ka siyo sarƙar nan?" "Eh what happen?" Ɗaya hannun dake cikin nashi ta kwace tare da cewa "yaya million biyu da rabi fa" "Yea! Da kyar ma na samu wannan ɗin shiyasa kikaga na daɗe ban dawo ba inata yawo inason wadda tafita tsada amma ban samu ba." "Amma yaya million biyu da rabi fa! Marayu nawa za'a farantawa rai da wannan kuɗin? Shine ka siyo min Abin wuya kawai inyi ado dashi?" Haƙiƙa Nawaz tana birgeshi sosai, tausayinta da sanin ya kamata ɗin ta yana birgeshi "okay to yanzu kada ki damu, zan samu lokaci saiki lissafa min marayun da kikeso a farantawa rai, but wannan nakine saboda faranta nawa ran da kikayi, diamond ne da pearl aka haɗa su guri ɗaya, kece farkon Wadda ta fara sa irinta a wuyanta, Royal design ce" Shiru Kawai Nawaz tayi tana duba wannan lamari, "to waishi Aayaan wane irin mutum ne? Haƙƙin shine fa ya amsa, amma sai wani gode mata yakeyi yana mata hidima" Shima ganin Nawaz ɗin tayi shiru, sai yaci gaba da tuƙinshi yana Nazarin yanayin ta, sam bata ɗauki duniya da zafi ba, yasha ganin abokanshi sun siyo wa matansu abu amma memakon suyi godiya sai su kushe abun suce beyi musu ba ko suce tsohon yayi ne ko kuma ba irinshi suke so ba. Amma ita Nawaz ko me ya bata saita nuna mishi farincikin ta a fili da ɓoye, ta riƙa godiya kenan tana mishi addu'oi. Sun ɗauki lokaci me tsawo a haka inda Aayaan ya kamo hannunta ya matsa a hankali, ɗago kanta tayi suka haɗa ido, da sauri ta kauda kai domin kunyarshi take matuƙar ji. "Sweetheart tunanin me kike yi?" "Rayuwata nake duba yadda ta koma sanadin SARFRAZ" "Inaso in samu lokaci na musamman ki ƙara bani full labarinki, inaso naji usulin wacece MADINATUL MUNAWWARAH wato my beloved wife" "Kada ka damu anytime ka shirya just let me know, zan faɗa maka komai In'sha Allah" Murmushi yayi ya jinjina kai Alamun ya gamsu da maganar ta, wani gurine babba iya ganinka, a kewaye yake da fencing wire dai Babban gate shima na wire, ciki Aayaan ya shiga da motar yaci gaba da tafiya, Saida yayi tafiya mai nisa a cikin gurin Sannan yayi Parking dai dai wata kasan bishiya. Shiru gurin babu alamun kowa illa allon koyar harbi me suffar mutum wandanda da suke jere a jikin wani gini. "Dear kinga inda zan koya miki Harbin, hope zaki bani haɗin kai, kuma pls ki cire tsoro" Murmushi Nawaz tayi, ita dai tunda yace mata zai koya mata harbi taji zuciyarta na bugawa da sauri da sauri, amma tanata danne wa saboda kada ta ɓata mishi rai. Bayan sun fito ne ya zagaya baya ya buɗe ya buɗe Boot tare da ciro wani akwati baƙi me faɗi, bindigogi ne kala kala acikin da bullet harda su salansa, zare ido Nawaz tayi tare da cewa "yaya duka wadannan naka ne?" "Yea nawane! Ko kema kinaso in baki?" "Eh" Nawaz tace tanata murna, shikam Aayaan ganin Irin farin cikin da Nawaz keyi yasa yake jinshi cikin annashuwa, sai murmushi yakeyi. Komai ya haɗa na bindigar inda daga bisani ya janyo Nawaz cikin ƙirjinshi Tare Da ɗora hannuwanta saman bindigar sannan ya ɗora nashi daman nata, sosai yake nuna mata Yadda zatayi, sunfi ƙarfin awa ɗaya suna abu ɗaya. Sakinta yayi ya miƙa mata bindigar Tare Da cewa harba mugani, Rufe ido Nawaz tayi zata harba, da sauri ya dakatar da Ita tare da cewa "sweetheart buɗe idonki! Idan kika rufe idonki bakisan inda zaki harba bullet ɗinba, buɗe ido Nawaz tayi a hankali Sannan ta saita bindigar tare da harba kunamar, a daidai 80degree bullet ɗin ya faɗa, wani irin tafi Aayaan ya sakin mata tare da fitoo yana cewa well-done, gwajin Farko, gaskiya naji daɗi sosai, nasan ko sati baza muyiba zaki fini iyawa. Sosai Nawaz taji wani kwarin gwuiwa ya shigeta, take ta nemi tsoron datakeji ta rasa saboda yadda taga Aayaan yaji daɗi sosai. Maida komai yayi cikin akwatin Sannan ya maida Boot ɗin, beverage pack ɗin dake ajiye a cikin motar ya ciro waje tare da ɗaukar carbonated drink yanasha, Hannu Nawaz takai zata dauka itama, ai da sauri Aayaan ya ɗauke kwandon, miƙo mata milk drink yayi tare da cewa "Ai daga yau babu ke babu kuma shan carbonated drink har saina gama observing ɗin danake yi a kanki," Amsa tayi bata ce mishi komai ba. Ƙaramin carpet ɗin dake cikin motar ya ciro ya shimfiɗa ya zauna a kai, janyo Nawaz yayi saman cinyarshi Sannan ya ciro wayarshi dake aljihun wandonshi. Number Aseey yayi dialling, ringing ɗin farko ta daga da jaraba "Malam meye na kirana, aini na yafe ka tunda baka damu daniba, ko ka nemeni, na rasa Yadda zanyi da raina duk sanda zan kiraka switch off kuma kai kaki kirana, idan na kira Mummy itama ta rufe ni da faɗa wai ina so na dameku, fisbilillah yanzu fa kusan kwananku arba'in amma ko ka nemi wani, wai dama haka honey moon ɗin yake? Baka tunanin ka shiga haƙƙin Sis Nawaz ɗin kummm....... "Calm down! Calm down, yanzu bansan wane laifi zan amsa ba, don Allah kiyi haƙuri, Nasan nayi laifi amma gani nayi nima babu wanda ya kira yaji ya muka sauka shiyasa nima ban kira kowa ba" Sanyi jikin Aseey yayi, tabbas Aayaan be taɓa yin hakaba, kuma su kansu be kamata ace ya tawo da ƴar mutane amma babu Wanda ya kira yaji ya suka sauka, "bro to amma dakaga ba'a kiraba kai ai saika kira?" "Nifa gani nayi kamar an gaji dani ana neman kai danine" "Kai sweetbro! Wane irin an gaji dakai? Yanzu fa wani irin muhimmanci ka kara a idon kowa, kazama magidanci, where is my sis?" "Gatanan bama tajin daɗi " Daɗi ne ya kama Aseey tana tunanin ko ƙaramin laulayi Nawaz ta fara " bata wayar" A kunne ya kanga wa Nawaz wayar Tare da cewa "yi sallama" "Assalamu alaikum, barka da Rana Aunty" "My dear nayi kewarki sosai, fatan kina lafiya? Ya ƙarfin jikin naki? "Nima haka Aunty, nayi kewarki sosai da Muhsin, yana ina? "Be dawo daga school ba" "Don Allah Aunty yaushe zakizo" "Idan kun gayyaceni, kuma nace miki ya jiki baki bani amsa ba" "Aunty ba wani ciwo bane, zazzaɓi ne fa kawai kuma naji sauki!" "Okay to Allah ya ƙara sauƙi, and kuma yayi maza ya kaiki Asibiti kada ayi sake" Haka dai suka ɗanyi hira inda Aseey ta daɗa jaddadawa Aayaan cewa ya tabbatar ya kira Mummy da Ummin Nawaz don jineya suke!" Yana kashewa ya kira wayar mummy akashe, kiran wayar Ummin Nawaz yayi, koda ta ɗaga da sallama kasa amsawa yayi sai ya miƙawa Nawaz wayar tare da cewa "Ummu ce" Fashewa da kuka Nawaz tayi tare da cewa "ummina nayi kewarki sosai" "Jimin shirme! Yanzu Madina kuka zaki kirani kina Min" Mummyn Aayaan dake gefenta ne ta amshi wayar tare da cewa "my dear meya faru? Ko wani abun yayan naki yayi Miki?" "Ina wuni Mummy " "Lafiya Lau my daughter, ya kike?" "Lafiya Lau Mummy " "To faɗa min meyayi Miki" "Mummy wallahi bemin komai ba, Kawai dai nayi kewar kune" "To stop crying! Zansa ya kawoki konji" "To mumy Nagode " Miƙawa Ummin Nawaz wayar tayi, namma dai nasiha tayi mata suka ɗan tattauna Sannan akayi sallama suka kashe wayar. "Kuka kuma dear? "Kayi haƙuri, Wallahi inajin muryarta naji kukan yazomin. "Okay to stop cryingy, ɗauki madararki ki shanye" Cigaba dashan madarar tayi tana ɗan tunani ahankali. Saida ya tabbatar ta shanye sannan ya goge mata baki da tissue ya bata Ruwa. A gurguje suka biya Asibitin haidar ɗin inda Aayaan ya faɗa mishi Irin magungunan da yakeso aba Nawaz. Dariya haidar yayi tare da cewa "dama wannan lodin da kayi na shekaru idan ba'a samu ribaeda wuri ba ai anyi asara" "Dalla malam kabani Abinda nace kabani, banson munafurci! "Iyyeh! Dayake na gama nawa amfanin Koh? To ai Shikenan " Koda suka fito zasu tafi yana kallon Yadda Nawaz ta zubawa motar haidar ido al'amurra bata sha'awa, daga karshe ma saida ta taɓa seat ɗin, dayake Irin me budadden saman nance. Sallama sukayi da haidar suka kama hanya, "Madam motar haidar ta baki sha'awa!" "Ya akayi ka sani " "Nasan duk abinda kike so ai" murmushi Nawaz tayi tare da cewa wallahi ta burgeni ne sosai kuma dama ko a cikin film naganta ji nakeyi kamar na shiga cikin TVn na ɗauko. "Don't worry, kisa a cikin ranki kema nan da 30mins kinada irinta!" Zaro ido Nawaz tayi "me kake nufi" "Just keep quiet and see" Ita dai Nawaz shiru tayi tana tunanin me Aayaan zaiyi. Be tsaya a ko ina ba sai wani Babban gurin da ake siyarda motoci, magana sukayi da baturen ta Yan mintoci, sai suka bi wata hanya, dayake ita Nawaz an bata kujera ta zauna. Ko minti Bakwai ba'a yi ba, saiga su a cikin irin motar haidar komai da Komai. Da sauri Nawaz ta Miƙe tana yiwa Aayaan kallo me cike da tambayoyi. *BAYAN SATI SHIDA.....* Abubuwa da yawa sun faru, wanda daga ciki zargin Aayaan na tunanin Nawaz ta samu ciki tun a Daren su na farko ya tabbata, don yanzu haka ɗauke take da ciki na sati shida amma ita bata saniba, ga wani irin mugun barci da takeyi kamar kasa, kuma sam batada abinci sai nama da Madara, ko hatsi bata yarda taci sai Aayaann yayi da gaske tukuna. Makarantar ma ta jingine ko maganarta bata yi, su maman sudeis sunyi bikon har sun gaji.. Sun ziyarci Aseey, sannan Aayaan yayiwa maman sudeis kyautar mota KIA kerato ita da Fatima. Koda wasa Nawaz bata taɓa kawo cewa ciki garetaba, sosai wata irin shaƙuwa ta kamasu ita da Aayaan, bata iya rintsawa idan ba a cikin ƙirjinshi ta jita ba, kowane motsi so takeyi tajita a kusa dashi, sosai takeson kamshin jikinshi. Misalin Bakwai da rabi na safe Nawaz ta farka da wani Irin mugun mafarki, tunda ta tashi Aayaan ya lura tana cikin damuwa, sosai yake tambayarta meya faru amma sai dai tace mishi Babu komai, kuma data kalleshi sai idonta ya cika da hawaye . Kuyi haƙuri da typing errors yauma banyi Editing ba🥱 *MATAR RASHEED ✍️**🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *78* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Yayi yayi ta faɗa mishi menene amma sai tace babu komai, daya matsa mata sai ta fashe mishi da kuka tana cewa "yaya don Allah kada ka rabu Dani, Wallahi na dena yi maka musu, kuma duk abinda kakeso zanyi maka" Lallashinta ya fara yana cewa "dear Nothing will happen In'sha Allah, we will live together, ko a cikin aljannah ke nake fata ki zamo min mata, babu abinda zaisa na rabu dake in'sha Allah " "Promise bazaka barni ba" "I promise to be together in'sha Allah, tare zamu raini cikinmu, kuma tare zamu haihu don bazan bari wani ya gan mini Naƙudar mata ta ba" Shiru Nawaz tayi domin maganar da Aayaan yayi ta karshe ta bigeta, kenan ciki gareta shiyasa komai nata ya canza? Farin ciki taji a maimakon taji fargaba, "yaya da gaske ciki gareni?" Mamaki ne ya kama Aayaan ganin Nawaz tanata farinciki, be taɓa tunanin haka Abin zai zo mishi da sauƙi ba, ai da tuni zai faɗa mata, ya zaci zata shiga damuwa ne idan taji, "Kinaso ne?"Aayaan ya tambayeta "Eh ina so, amma me kama dakai kuma sunanka nakeso asawa jinjirin" Rungumeta yayi yanajin wata irin ƙaunarta har cikin ruhin shi, sosai take bashi tausayi saboda cikin data samu cikin gaggawa, sam bata huta ba, danma Allah yasa laulayin na kwadayi ne bana ciwo ba. "Kinsan wani abu kuwa? "A'a" Cewar Nawaz tana daɗa shigewa cikin jikinshi "Nifa kunya nakeji a ganki da ciki, nasan kowa cewa zaiyi ɗan ƙaniya, yayi aika aika" "Hmmm balle ni kuma, don Allah kada ka faɗawa su mummy da Aunty Aseey" "Kai! Ni dana ke jin kunya ta ina zan iya faɗa? Sai dai ko ke" "Rufamin asiri Nima Wallahi bazan iyaba. Ahaka suka wuni suna hira, sai dai har zuwa lokacin zuciyar Nawaz cike take da fargaba, tsoro takeyi kada abin data gani a mafarki ya zama gaske, idan haka ta faru ta shiga ukunta, bata san inda rayuwa zata kuma jefata ba. "Dear yanzu ace na mutu zaki iya Auren Sarfraz?" Tambayar da Aayaan ya jefowa Nawaz kenan Idonta ne ya cika da ƙwalla "kaga ka dena min maganar mutuwa a gurin nan, meye na zancen wani Sarfraz? To bari kaji wanima bazan iya aureba balle Sarfraz, banda ra'ayin kowa face kai." Sanyi Aayaan yaji har cikin ranshi jin cewa matarshi na sonshi "to misali na mutu kafin ki haihu, idan kika haihu zaki iya ba mummy ɗan da kika haifa ko zaki riƙe ne? Fashewa da kuka Nawaz tayi tana tuna mafarkinta, cikinta ta shafa tare da kama hannun Aayann tana ɗorawa a saman cikin "kayi alkawarin cewa tare zamu raini ya'yan mu, mu basu tarbiyya me kyau " "Nayi miki alkawarin hakan, hatta rainon cikin bi'iznillah tare zamuyi shi" "To yaya don Allah ka dena maganar mutuwa duk da nasan tana kan kowa, amma kada ka manta yanzu fa kaine bango na kuma majingina ta, idan ka mutu ya kakeso nayi, to aini kaina yanzu Yar gidan mummy ce balle Abinda na haifa." "Nevermind we will die desame day in'sha Allah, hope U Are happy now" Murmushi Nawaz ɗin tayi tare da cewa "yea i am Happy " Rufe bakinta keda wuya wayar Aayaann ta fara ƙara, koda ya duba sunan "colonel ya gani " Da sauri ya ɗaga yana mamaki saboda ɗazu suka gama waya dashi "hello Sir" "Aayaan kiran ujila ne daga sama, gobe da yamma ake buƙatar mu isa ƙasar Ukraine, muna daga cikin special soldiers guda ɗari biyar da aka zaba cikin ƙasashen duniya wadanda zasu kai musu agaji." "Okay sir I will be getting ready in'sha Allah " Kashe wayar colonel yayi bayan ya daɗa jaddadawa Aayaan ya tabbatar gobe sun haɗu a inda akace su haɗu. Sosai fuskar Aayaan ta nuna damuwa bayan ya gama wayar, "dear kinji wai kiran ujila akayi mana daga sama, wai zamuje mu kaiwa kasar Ukraine agaji" Zumbir Nawaz ta Miƙe tana tuna mafarkinta, kada fa gaskene Aayaan mutuwa zaiyi ya barta, domin mafarki tayi wai yaje yaƙi Wata ƙasa sai gawarsa aka Kawo ya mutu. Tashi tayi ta daka tsalle "wallahi bazai yiwu ba, nidai gaskiya baza kaje ba, gaskiya ka nemi uzuri Ni zuciyata bata kwanta min da tafiyar nan ba, tana kaiwa nan ta fashe da kuka tana yarfa hannuwanta. Da sauri Aayaan ya miƙe shima tare da riko ta yana cewa "sorry ki natsu pls, ji yadda kike tsalle, ko kinaso kiyi ɓarin me kama ko ince takwaran Aayaan dinki ne? Tafiya Ukraine bashi ke nuna miki zan mutu ba, addu'a Kawai zakiyi Allah ya dawo miki dani lafiya" "Wallahi ni banson kaje, pls ka taimakeni kada ka rabu Dani?" "Dear don't worry I promise zan dawo gareki cikin koshin lafiya muci gaba da rainon cikinmu Koh? "Nifa zuciya ta tsinkewa takeyi tun ɗazu" "Babu Yadda zanyi ne amma dana fasa zuwa, but nayi rantsuwa akan zan kare rayukan al'umma iya ƙarfina, so Please kimin addu'a kawai" Babu yadda Nawaz zata yi ne amma tunanin Yadda zata bar Aayaan ya tafi wata ƙasa yaƙi takeyi bayan tayi mafarkin ya mutu yana yaƙi, fashewa tayi da kuka wiwi, don yadda takeji a jikinta tasan ba Lallai su kuma haɗuwa da juna ba idan ya tafi. Babu yadda Aayaan beyiba amma taƙi yin shiru, yayi yayi amma babu improvement, sai Kawai ya kira mummy ya miƙa mata wayar. "Daughter lafiya kike kuka" "Mummy yaya Aayaann ne wai zai tafi yaƙi ya barni" "Iyye to be isa ba, babu yadda za'a ayi ya tafi ya barki a ƙasar da ba taki ba, bashi wayar" "Hello mum ina yini?" "Banson gaisuwarka, maza yanzu kayi booking flight, Kafin ƙarfe huɗu na yamma ka tabbatar ka kawo min ita gida, idan yaso sai ka tafi duk inda kake so!" Ba haka Nawaz taso ba, taso ace mum tace mishi kada yaje ne amma ba wai ya maida ita gida ba. Koda ya kashe wayar sai yayi shiru, duk jikinshi yayi sanyi yana tunanin yadda zai iya barci ba tare da Nawaz na cikin jikinshi ba, saboda yadda yayi sabo da hakan. Haɗa Duk wani abu da yasan zata buƙata yayi a cikin luggages ɗinsu, sosai yake cikin damuwa kuma ya rasa dalilin shiga damuwar tashi. Gidansu maman sudeis da fatima ya kaita sukayi sallama Sannan ya wuce dasu gidan haidar. Misalin shabiyu na rana suka isa airport ɗin, ita dai Nawaz kallon komai takeyi kamar a mafarki, tana yiwa ƙasar kallon ƙarshe ne, gashi Aayaan yabar komai a apartment ɗinsu yace inya dawo zaizo ya ɗauketa su komo, harta motar ta tana chan gida. Tana zaune a seat ɗinta ne amma ruhinta is nowhere, wani Irin abu takeji ya tokare mata ƙirji, shikuma Aayaan duk saiya ƙara shiga cikin damuwa ganin yadda Nawaz ɗin ke cikin ƙunci. Tanajin sanda ake sanar da cewa jirgin zai tashi sai kawai ta rufe ido kamar tana barci. Ganin hakan da tayi yasa Aayaan ya rabu da ita, saboda shima bawai daɗin jikinshi yakeji ba kuma ya lura itama kamar batason damu. *Bayan kyawawan awanni huɗu da rabi....* Nawaz ce riƙe da Aayaan tana zunduma ihu akan ita wallahi bazai tafiba, ko kuma ya tafi da ita, Mummy ta rasa yadda zatayi, daga karshema Mummy ce tace "Ni Wallahi danasan Abinda zai faru kenan da banyi gigin cewa ku sauka a nan Maidugurin ba, da cewa nayi ku sauka a chan zariya nima nai zamana achan, Nasha wahalar zaman mota ne amma da Yanzu zamu koma chan ɗin" "No mum please kiyi haƙuri ku zauna Anan ɗin, idan ma kina ganin akwai damuwa Ni zan kira mijin Aunty Aseey in nemi Alfarma ya barta ta tawo saboda shima yau kwana uku kenan da yatafi Dubai, zansa ayi mata booking ɗin Flight gobe da safe in'sha Allah. Ita kanta Mummyn cikin ƙunci take jinta gashi ta rasa meke damunta, zuciyarta sai bugawa takeyi da karfi, ga fargaba da zullumi kuma Batasan dalili ba. Ɗaukar Nawaz Aayaan yayi ya shiga ɗaki da ita, a saman gadonshi ya ɗora ta "yanzu dear dama duk yadda nake dake a matsayin makaryaci kike kallona" Cikin Muryar kuka tace "A'a wallahi ina yarda da duk Abinda ya fito daga bakinka" "Banga alama ba, tunda babu irin alƙawarin da banyi miki ba akan cewa zan dawo gareki ba, amma kinki yarda, nace miki bazan taɓa mutuwa na barki ba sannan kuma bazan yarda kema ki mutu ki barni ba" Kama hannunshi tayi tace "na yarda da kai, Allah ya tsareka ya dawo dakai lafiya cikin amincin shi, kada ka manta cewa kabar matarka da danka achan wata uwa duniya, so Please take good care of yourself, *I LOVE YOU, AND I PROMISE TO LOVE YOU TILL MY LAST BREATH* " Sosai Aayaann yaji daɗin kalamanta, besan sanda ya rungumeta ba kamar zai maida ita ciki. Komawa tayi ta kwanta don bazata iya rakashi ba. Mummy dake tsaye a falour tayi mamakin ganin Aayaan ya fito ba tare da Nawaz ba "son ina daughter na take?" "Ta haƙura, tana chan ta kwanta" "To Nagode, Allah yayi maka Albarka, kuma ya dawo mana dakai lafiya" Sumbatar goshinta yayi tare da cewa "Ameen, mum" Har bakin mota ta rakashi inda duka securities suka shiga sukai gaba, har Saida suka fita daga gidan Sannan Mummy ta koma ciki. Mamaki takeyi har yaushe Nawaz ta saba da Aayaan haka, Kodayake ba'a shiga tsakanin mata da miji ai. Kunya sam ta hana Nawaz fitowa gurin mummy, ga kunyar surukunta ga kunyar abinda tayi ɗazu. Sai wajen bayan magrib mummy ta haɗa abinci ta tafi kaiwa Nawaz ɗin, tasan kunya ce kawai ke ɗawainiya da ita shiyasa ta kasa fitowa, kuma be kamata ta barta batare da ta ci abinci ba saboda ta lura akwai sabon ciki jikinta. Koda mum ta shiga ɗakin Nawaz ji tayi kamar ta zunduma da gudu, da sauri ta zame ƙasa tare da cewa "barka da dare mum" "Tashi tashi, kada ki kuma duƙawa, keda ba daɗin jikinki kikejiba, yanzu shiga bathroom ki daurayo bakinki da hannunki kizo kici abinci" Cikin sanyin jiki Nawaz ta tashi ta shiga bathroom ɗin, sai bayan kamar minti huɗu ta fito, zama tayi a ɗan nesa da mummy ta duƙar da kanta. "Dawo kusa Dani" Ƙara matsawa tayi amma ba sosai ba, "daughter pls ki ɗaukeni kamar umminki, pls kada ki riƙa boyemin komai, and pls kada ki kuma hora kanki da yunwa dan Allah!" "To mummy in'sha Allah, Nagode sosai" "Nevermind babu godia tsakanin mu, yanzu ki damu kici abinci zan dawo anjima na duba ki" "To mummy! Abinda Nawaz ta iya cewa kenan ta kuma duƙar da kanta. °°°°°°°° *Washegari.......* Misalin ƙarfe biyar Aseey ta dira a Maiduguri, sosai mummy taji daɗin zuwan ta saboda ko banza Nawaz zata ɗan rage damuwa. Barin ga Muhsin ma, tunda ta santa da son yara. Wayarta ta nemo ta kunna tare da jona ta a chargy, Aseey na gefe tana murmushi "hala Aayaan zaki kira" "No Aunty ai baza'a iya kiranshiba sai dai shi ya kira mu" "Au na manta Nima da mukayi waya jiya ya faɗa min haka" Kwanciya Nawaz tayi tare da ɗaukar wayar, gallery ta duba inda ya tura mata photunan shi tun zuwansu Zaria na farko, photon ta zubawa idanu tanajin kamar ta fito dashi yayi mata magana, tanaso taji muryarshi, tanaso ta ganshi, tanaso taji duminshi amma babu hali, numbobinshi taketa dialling amma babu wadda ta shiga. Message ta shiga tafara tsara mishi sakon karta kwana, ta tura mishi message sunfi goma kuma duk na ya tabbatar ya dawo gareta, kuma ya tuna da alƙawarin su. Yau kwana biyu kenan da tafiyar Aayaan, ko sau ɗaya be taɓa kiran suba, kuma suma duk kiran da zasuyi baya taba shiga, tun Nawaz na iya ɓoye damuwarta harta kasa ta fito da ita fili. Mummy da Aunty Aseey ma duk sun shiga damuwa, amma ganin Yadda Nawaz ɗin ta tada hankalinta sai su suka danne tasu damuwar. Yau ya kama kwana uku da tafiyar Aayaan, misalin ƙarfe huɗu na asuba, zaune Nawaz take saman dadduma tana ta addu'oi, wayarta ce ta fara ringing, da sauri ta miƙe ta ɗauki wayar a saman gado, fargaba da tsoro ne suka kamata ganin sunan dake lilo a gaban wayar. Tunanin ɗauka takeyi kada taji Abinda zaisa zuciyarta ta buga, tun Kafin ta ɗaga kiran ta fara kuka.... Yauma dai banyi Editing ba🥱 *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *79* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Naso naba *Amina Haruna* (meenash cool) wannan shafin amma na fasa domin faɗa zamuyi idan ta gama karantawa😭😭😭😭😭" *WANNAN SHAFIN NA SADAUKAR DASHI GA DUKA MASOYA SARFRAZ DA MAƘIYAN AAYAAN* A Hankali ta kanga wayar a kunnenta, sannan cikin kuka tace "Hello daddy" "Haba sweetheart! Har yanzu dama baki haƙuraba!" Muryar Aayaan tayiwa Nawaz amsakuwwa a cikin kunne "Saida ta cire wayar a kunnenta ta kuma kallon screen ɗin wayar inda *Daddy Colonel* ke rubuce ɓaro-ɓaro. "Maman little Aayaan! Pls talk to me" Aayaan ya kuma cewa "Ba kai bane kaƙi kiranmu, kuma ko mun kiraka bata shiga" "Don Allah kiyi haƙuri sweetheart, dukanmu waɗanda aka sa cikin list ɗin waɗanda zasuyi aikin datse mana network akayi daga sama, wai ba'a so a san inda muke" "To yanzu ya akayi ka kira da number dady" Nawaz tace cikin Muryar shagwaɓa "Zancen da tsawo amma bari na yanke Miki, Ashe duk wannan ɓoye-ɓoyen da nakeyiwa Colonel akan aurenmu kallona yakeyi yasan komai, wai Ashe duk Abinda akayi sai Mummy ta kirashi a waya ta sanar Dani, Kinga faɗan danasha agurinshi kuwa, hmmm yanzuma shi ya bani wayar wai na kira ki naji yadda kike" "Allah sarki dad, naji daɗi daya nuna kulawa a kaina, to yanzu ya kake? And please kada ka kuma ɗaukar lokaci me tsawo Irin haka baka nememu ba" "Kema kinsan ai bana lafiya tunda bana tare dake, and in'sha Allah i will try my very best wajen kiranku akai akai." Daɗi Nawaz taji sosai, "yaya Please ka kirani video inaso na ganka" "Kamar kin shiga zuciyata, Nima ke nakeso nagani, oya shiga app ɗin yanzu Zan kira" Yana katse kiran ta shiga Skype da sauri, shigarta keda wuya saiga kiran shi yana shigowa. Da sauri ta ɗaga tare da kallon cikin wayar sosai, ganin Aayaan tayi kamar ba Shiba, saboda yasa irin hularnan me kama da ciyawa Sannan ya shafe Fuskarshi da wani baƙin abu. "Yaya ya naganka haka" Nawaz tace kamar zatayi kuka. "Mun shirya ne saboda nan da awa ɗaya zamu fita, kuma kinga nine commander dole na shirya da wuri" "Ya zanyi! Zanta yin addu'a har Allah ya taimakeni ya dawo min dakai gida lafiya, to Amma a ina kake naga haske a ko'ina" "Ina cikin barrack ne, amma sweetheart naga kamar kin rame?, Zamu ɓata fa idan kika wahalar min da kanki keda little Aayaan" "Ni bana iya cin abinci kuma ko barci bana iyawa, burina kawai in ganka, inji duminka da kamshin ka" "Oh my gosh, yanzu dear dama bakya barci? Ko abinci bakya ci? Ya kikeso nayi to? So kike zuciyata ta buga?" "Inaci amma kaɗan, saboda bakina ɗaci " "Okay to zansa securities su riƙa yi miki order a chicken republic kullum har zuwa In dawo'' "To Nagode, amma mummy ma tana ƙokari sosai akaina, kawai na kasa jure Rashin ganinka ne" "I'm sorry sweetheart, I promise to be back soon in'sha Allah, Aunty Aseey ta iso Koh" "Eh tazo, amma saita riƙa cewa wai ciki gareni! Tai ta tsokana ta Tanaso ta hanani fitowa falour, kuma ni kunyar Mummy nakeji" "Oooh dear rigima! So don tace ciki gareki what's there? Itafa Ɗa gareta karewa" "No ni banso mummy ta san komai, nifa kunyarta nakeji Allah" "To Shikenan I'm sorry, a taimaka a budemin Little Aayaan mu gaisa!" Ƙasa tayi da wayar dai dai cikinta Sannan ta yaye rigar, kiss Aayaan yayi ta cikin wayar tare da cewa "little Aayaan hope zaka jirani harna dawo, And pls a taimaka adena ba mummy wahala! Idan na dawo sai a cigaba saboda kada abin yayi mata yawa" kiss ya ƙara yi Sannan yace "i love You dear" Ɗago da wayar Nawaz tayi tana murmushi "sai aka ce maka ciki yana jin magana Koh?" Murmushi shima Aayaan ɗin yayi tare da cewa "hmm yana jina mana, kuma ki bari kigani bazai wahalar dake ba har zuwa in dawo in'sha Allah" Sun ɗan ƙara hira sosai inda a ciki Aayaan yaketa rokon Nawaz akan ta kwantar da hankalin ta, kuma kada ta damu zai riƙa kiranta duk sanda ya samu time, ta ɓangaren Nawaz sosai ta samu relief akan damuwarta, koda suka gama wayar sai takejinta sakayau, bini bini tayita murmushi. Dai dai lokacin aka kira sallar asbah, tashi tayi ta tada iƙama dayake dama da alwalarta. Su kansu su mummy sunata mamakin yadda yau ta saki jikinta har hira suketayi, amma ada muhsin Kawai take kulawa, ko kuma tana ƙudunɗune a ɗaki. Kamar yadda Aayaan yayi alƙawarin zai riƙa kiranta, sosai yake kira ɗin saboda duk sanda ya samu dama koda ta minti goma ce saiya kira yaji ya take, Yanzu ma waya sukeyi inda yake ce mata " pls sweetheart kiyi min addu'a, yanzu zamu fita kuma i think wannan ce fitarmu ta ƙarshe don haka nasan Abin zaiyi zafi sosai" "Kamar ta zunduma ihu haka taji amma sai ta daure tace "to muna gama waya zan tashi nayi Alwala nayi nafila na roka mana Allah akan ya kare mana kai, kuma yasa ka fita a Sa'a, zan faɗawa Mummy ma" "To Nagode sosai sweetheart, yau dai ammin rowar little Aayaan Koh?" Murmushi tayi tace "idan ka kuma kira zan haɗa ku" "Dear kinsan me! idan na kira mummy cewa takeyi ta yafe, wai tafison na kiraki saboda idan kika shiga damuwa basa iya Miki, Amma idan kina cikin farin ciki kowama haka zaki ganshi cikin kwanciyar hankali" "Hmmm Mummy fa tace wai ita yanzu Yar kallo ce, wai nafi sonka" Kyalkyalewa da dariya Aayaan yayi harda tafa hannu "Allah Sarki mummy, in'sha Allah idan mun samu yadda mukeso zuwa jibi ina gida, Kinga sai a raba gardama Idan na dawo, and kuma pls and pls banson wannan rakin naki domin tarba kakeso kimin ta musamman, saboda i really miss your warmth. Murmushi Nawaz tayi "To Allah ya dawo mana dakai lafiya, kuma kada ka damu i promise zakasha mamaki" Sosai Aayaann yakejin daɗin yadda yanzu Nawaz ke kula dashi, kuma da alamu kunyar ma ta ragu sosai. Cikin farin ciki suka gama wayar, kwanciya Nawaz tayi ta lula duniyar tunani, sosai take tunanin tun randa ta fara haɗuwa da Aayaan a daji, yadda ya ɗauketa har zuwa inda ya Kawo mata tea, da Ruwan Alwala daya kawo mata ya yaga zanin gadonshi biyu ya bata tayi sallah, tsokanarta da yake yawanyi, zallar ƙaunar da yake nuna mata a fili, tsabar saboda beson ya cutar da ita sau ɗaya ya kuma kwantawa da ita tun bayan First night ɗinsu. Hawayene taji zuna zuba ta idonta, da sauri tasa hannu ta goge tare da cewa "Allah na roƙeka ka taimaka ka dawo min da mijina lafiya, Wallahi nayi alƙawarin zan bashi dukkan wata kulawa, kuma zan tarairayeshi kamar jinjiri" Tashi tayi ta shiga bayi ta dauro alwala, tana cikin Sallah Aseey ta shigo, ganin Nawaz ɗin tana Sallah sai ta fita kawai. Koda Nawaz ɗin ta idar da Sallar zama tayi taita addu'a Daga busani ta mike ta fita falour zuwa gurin Aunty Aseey Saboda taji menene tazo ɗazu. Film ɗin Saif Ali Khan akeyi a Bollywood mai suna *phantom* an fassarashi da Hausa *Farmakin Adalci* Aseey na ganinta tace "zo ki zauna kusa dani, yau zamu sha kallo, yau Bollywood duk finafinan sojoji zasuyi, kinga idan aka gama wannan *Holiday* zasuyi, idan aka gama shi shima *Baghi* zasuyi.. Murmushi Nawaz tayi tana kara jin ƙaunar wannan ahalin acikin jininta, ya zama dolema ta saka musu da ALKHAIRI, kowa burinshi ya sata a Cikin farinciki. Sosai taji daɗin kallon Film ɗin, sai dai Inda ya ɓata mata rai da akace Saif Ali Khan ya mutu a ruwa har kuka tayi, kallon Aseey tayi tace "yanzu Aunty ya Nawaz Mistry zatayi" "Ohh Nawaz Film ne fa, to meye na kuka kuma?" Dai dai nan mummy ta fito " su Aseey kuka ma kika sata yi? Wato an samu taji sauƙi shine zaki dawo mana da hannun agogo baya! To ki kashe Kayan kallon nan ki tashi ki bani guri" "Mummy baf......... Kafin Aseey ta gama magana mummy tace "ko ki mayar min tashar CNN ko ki kashe TV ɗin duka" Remote Aseey ta ɗauka ta maida tashar zuwa CNN A tare suka miƙe ganin headline ɗin News ɗin... Jikin Mummy har rawa yakeyi ganin a gefen TV ɗin an rubuta *"AN JEFAWA SOJOJIN HAƊAKAR DA AKA GAYYATA DAGA KASASHEN DUNIYA BOMB, YANZU HAKA ANA HAƘO GAWARWAKIN WAƊAN DA BASU ƘONE BANE"* Nawaz kam daki ta koma da gudu ta dauko wayarta, kiran Number colonel takeyi amma switch off, ta kira ta kira harta gaji, sai kawai ta fashe da kuka ta fadi a ƙasa. Da sauri su Mummy sukayi kanta suna cewa "kiyi haƙuri sweetheart, yanzu fa aka fara News ɗin, ba lallai da Aayaan a cikin suba" "Wayyooooo Allah na shiga ukuna, wallahi Idan yaya Aayaann ya mutu nima mutuwa zanyi, wallahi ko ban mutu ba saina haukace, nashiga Uku! Na shiga uku ya zanyi da raina, wayyooooo wayyooooo" babu yadda basuyiba amma Nawaz taki yin shiru, gaba ɗaya jikinta yayi zafi sosai zazzaɓi ya rufeta. Doctor Aseey ta kira tazo ta duba ta tace jininta ya hau kuma bugun zuciyarta ya haura ƙa'ida Sannan ruwan jikinta yayi ƙasa. Allurorin barci tayi mata sannan ta ɗaura mata drip, inda tace zata dawo anjima. Su kansu ji suke yi kamar zasu daɗi saboda tashin hankali, zuciyoyinsu kamar zasu fashe tsabar fargaba, ita mummy ma gani takeyi ai gara Nawaz tunda har zuciyarta ta fito da Abinda takeji. Abu dai babu improvement saboda wayar Nawaz na hannun Aseey, ta kira yafi sau ɗari amma bata shiga, kuma lokacin daya saba kira har ya wuce. Sosai suma suka ƙara karaya, itama Aseey kasa jurewa tayi ta fara zunduma ihu "wayyo Allah na! Dan Allah, Allah ka taimakeni kada ƙanina ya mutu, Allah don Allah ka tausaya mana halin da zamu shiga, ya Allah kaga bamuda uba, Ayanzu Aayaan shine ubanmu, ga matarshi da danyen ciki, ya Allah kada kada Abinda ke cikinta ya zama maraya tun kafin a haifeshi, wayyooo mummy na shiga uku idan Aayaan ya mutu" "Mummy dake tsaye kamar gunki ji tayi itama kamar zata faɗi, samun guri tayi ta zauna "Aseey ku haɗu ku kasheni da baƙin ciki tun kafin a tabbatar ya mutu ko be mutu ba, yanzu fisbilillah nifa uwace, ko kuna tunanin zaku fini jin zafi ne? Yanzu ke da nake zaton zamu haɗu mu kwantar wa da baiwar Allan nan hankali shine kema kike zunduma naki ihun Koh? To kisani cewa idan cikin jikinta ya zube munyi biyu babu ko ɗaya, idan Aayaan din ya mutu cikin ne matsayin shi a gurin mu, idan ya zube kuma Shikenan babu Aayaan babu makwafin shi " Cikin jan majina Aseey tace "To mummy wallahi damuwa ce ta kamani ganin har lokutan daya saba kiranta sun Wuce har kashi biyu" "Ki shiga bayi ki wanke fuskarki ki fito kada ta tashi taga kina kuka, kinsan jikinta ƙara taɓarɓarewa zaiyi, kuma Ni yanzu burina kada wani Abu ya samu cikin nan." Koda Nawaz ta tashi daga barci abu gaba ya daɗa yi Domin cewa takeyi ita a kira mata Aayaan ko itama ta mutu, har fusge fusge ta fara wai zata sauka akan gadon, Allah ya taimaka daidai lokacin Doctor ta dawo shine aka ƙara yi mata wata allurar Barcin, tasa mata wani drip ɗin wanda zai wakilci abincin da bata ciba. Zuwa lokacin itama mummy ta karaya sosai, bayi ta shiga ta fashe da kuka tare da cewa "ya Allah ka duba halin da wannan baiwar taka take ciki, kuma muma ka dubamu ya Allah, nasan baka barin wani don wani yaji daɗi amma ya Allah mun tuba, ka taimake mu Aayaan ya dawo" Yau dai kwana uku kenan, babu Aayaan babu kiranshi babu Colonel babu kiranshi. Kowa yanzu karfin hali kawai yakeyi, itakam Nawaz kullum tana cikin allurar Barci, don a tashinta na ƙarshe window ta buɗe tace zata faɗa. Wayar Mummy ce ta fara ƙara, koda ta duba Number ƙasar waje ta gani, jikinta har rawa yake yi ta daga tare da karawa a kunnen ta. "Mummy please i am sorry to say, Ni colique ɗin Aayaan ne kuma team ɗinmu ɗaya, he is such a very nice man, caring, kindness, Love in fact he is the best person I have ever meet in life, what i want to say is that, Don Allah kiyi haƙuri, haka Allah ya tsara. Sunje wajen aikin da zasuyi a ƙarshe sai aka mamaye su aka jefa musu Babban bomb ta sama, kuma gaskiya mugun bomb aka jefa musu Irin wanda hayakinshi ma kawai kashe mutum yake yi. An duba daƙyar aka samu gawar mutun 79 a cikin duka adadin da suka tafi, amma cikin ikon Allah an samu harda Aayaan ɗin a ciki, sai dai koda akaje asibiti babu irin Binciken da ba'a yiba amma an tabbatar ya mutu, yanzu haka ance in kira in sanar miki da cewa yanzu zamo tawo da gawarshi nan Nigeria Saboda ayi mishi sutura kamar yadda addininku ya tanadar, I'm very sorry mum. Aje wayar mummy tayi a gefe sannan ta haɗa hannunta guri ɗaya tare da cewa "Alhamdulillah ya Allah, Nagode da Ni'imar ka agareni ya Allah," Sosai zuciyarta ta bushe neman wani abu wai kuka tayi ta rasa, inda ita kam Aseey miƙewa tayi tanata tsalle tana ihuuu (Rayuwa kenan, Allah sarki Aayaan)😭😭😭😭😭 Ɗaukar wayarta Mummy tayi tanata kiran Yan uwa tana sanar dasu Abinda ya faru, kan kice me duka ko'ina ya dauka, dayake Aayaan akwai sauƙin kai ga damuwa da mutane... Cikin awa uku gidan ya cika fam da da mutane kala-kala, dayake wajen ƙarfe takwas ya kirata ya sanar da ita mutuwar Aayaan ɗin, wurin ƙarfe 3:36pm helicopter ɗin daya ɗauko gawar Aayaan ya iso harabar da helicopter ke sauka a cikin gidan, koda aka fito da Aayaan a cikin akwatin da akeyi na karrama sojoji an nannade shi da tutar Nigeria, miƙewa kowa yayi yanaso ya taba kamar wata gawar sahabi.😭😭😭😭 Banyi Editing ba saboda ina cikin tashin hankali😭😭😭 *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *80* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* *Ina ƙara ba masoyan Aayaan haƙuri, kunsan shi littafi yadda yazo haka yake tafiya, ban taɓa zaton Aayaan yanada masoya ba sai jiya daya mutu, to haka ma a rayuwar duniya Akwai wanda zakaji baka son shi amma wata rana sai yazo yafi wanda kakeso ma, Saboda a sanda na kawo Aayaan cikin littafin nan kowa baya sonshi, kowa haushinshi yakeji, amma jiya naga zahiri*, *To saboda haka wannan ya zama Aya a garemu, idan zamuyi so muyi ɗan dai dai, haka idan zamuyi ƙiyayya itama muyi ƙadan* Kuma inaso Don Allah ku jure kuci gaba da karanta littattafin nan saboda akwai sauran darussa a gaba. Nima banso Aayaan ya mutu ba, Nagode 🙏🙏🙏🙏🙏. *NA SADAUKAR DA WANNAN SHAFIN GA AMINA HARUNA (MEENASH COOL) INA FATAN ZAKI YAFE MIN, SABODA KE BABBAR FAN ƊIN CAPTAIN AAYAAN CE, KUMA IN'SHA ALLAH NAWAZ ZATA HAIFA MIKI WANI SABON AAYAAN ƊIN* Haka akayi kama-kama aka shigar dashi Babban falourn gidan daƙyar, saboda Saboda yawan mutanen da suka cika gidan. Gaba ɗaya gidan sai ya daɗa rikicewa saboda yanzu kowa ya tabbatar da cewa Aayaan ɗin ya mutu, Mummy zaune kawai take kamar itace gawar Saboda komai na mutuwar mahaifin Aayaan Sabo ya dawo mata, itakam yanzu meye ya rage mata a rayuwa da bata ganiba, ta rasa iyaye a sanda take cikin tsumman goyo, ta rasa ƙanwarta MUMTAZ, tazo ta rasa mijinta, yanzu kuma ta rasa Aayaan, shiyasa kukanma nemanshi tayi ta rasa.... Aseey kuwa har suma ta riƙa yi, ummin Nawaz ce da mummyn Sarfraz suketa kula da ita saboda suma sun rigada sunzo, Sarfraz kam zuwa yayi ya ƙanƙame gawar Aayaan ɗin yana kuka. Allah sarki Nawaz, tanachan tana barcin maganin barci da Ayanzu ya zame mata kamar ruwansha, duk wannan abu da akeyi bata saniba, baffan Aayaan baffan Nawaz, da duk wasu dangi suna zaune kowa idonshi a kumbure Alamun sunsha kuka sun gaji, Baffa ma cewa yayi, "mutuwa dama Ni kika ɗauka kika bar Aseey da ɗan uwanta, tunda Ni yanzu me ya rage min cikin duniyar" Kowa saida maganar ta ƙara tayar mishi da hankali. Ɗaukar gawar Aayaan akayi aka shiga da ita cikin falourn mummy saboda Anan za'ayi mishi wanka, duk wani abunda ake buƙata wanda za'ayi Amfani da shi an riga an tanada, kamarsu sabulu, turare, kafur, ganyen magarya, auduga dadai sauransu. Cikin ƙasa da awa ɗaya an gama yi mishi wankan har ansa mishi likkafani, amma ambar iya Fuskarshi a waje saboda Yan uwa suzo suyi mishi addu'a kafin a kaishi makwanci shi. Koda aka tawo da mummy tafe take kawai kamar gunki, Aseey kuwa gaba ɗaya ta zabge lokaci ɗaya, duk gaban Aayaan suka tsuguna kowa da Irin addu'ar da yake yi mishi, Aseey kam faɗawa jikinshi tayi, shima SARFRAZ daka ganshi zakaga ya koma kamar wani mahaukaci. Dai dai lokacin Nawaz ta buɗe idonta, bata jira kowa ba ta fige allurorin dake jikin hannunta tayo waje da sauri, don itafa baza tayi ta zama a cikin gidan nanba ba tare data san matsayin da Aayaan yake ciki ba. Fitowar da zatayi taga mutane da yawa a cikin falourn ga mutum kwance samɓal da likkafani, zuba wa gawar ido tayi, Aayaan ta gani cikin likkafanin idan ba gizo idonta keyi mata ba, jitayi kamar ta zunduma da gudu ta faɗa kanshi amma kafin tayi yunkurin yin hakan saboda yadda jikinta yake babu kwari taji baffa yana cewa "to yanzu a taso matarshi itama tazo tayi mishi addu'a kafin a kaishi gidan shi na gaskiya" Mummy ce tace "baba Don Allah kada a tasheta, wallahi idan aka tasheta komai zai iya faruwa, Saboda tun bata san ya mutuba muke fama da ita balle yanzu taga gawarshi shimfiɗe" Ahankali taja jikinta ta koma cikin ɗakin Aayaan ɗin da a yanzu ya zama nata, saboda tunda ya tafi a ciki take zaune, dayake duk sun bata baya basu ganta ba kwata-kwata. Drowar dataga ya ajiye bindiga sanda suka dawo daga England ta buɗe, ɗaukar bindigar tayi ta buɗe cikinta don ganin ko akwai bullet a ciki, cikin iKon Allah taga Akwai bullet har guda bakwai, batayi Wata wata ba ta saita bindigar tayi falour da sauri. "Kowa ya tashi ya fita ko na harbeku dukanku! Wato Ni kukeso ku cutar kuje ku binne min miji alhalin be mutu ba ko? "Mummy ce tace kunga abin da nake faɗa muku Koh? Wallahi Nawaz ba'a cikin hayyacinta take ba" Ummin Nawaz ce tace "Sarfraz Don Allah taimaka ka ƙwace bindigar hannnunta kayi ƙoƙari ka shigar da ita ɗaki ka rufe" Saita bindigar tayi dai dai kan Sarfraz "Wallahi idan ka matso kusa Dani saina harbeka" Kawu ne yace dalla can ka wuce ka kamata ka rufeta a dakin, kamar yadda ummin tace, don naga da alamu bazata bari a fita da gawar nan lafiya ba idan ba rufeta ɗin akayiba, mu zatayi wa barazana da wata fankon bindiga, ko yaushe ta iya harbin ma oho? Jin Abinda kawu yace *wato bata iya harbi ba* take Nawaz ta saita bindigar dai dai BABBAN TVn DAYA MAMAYE BANGO DAYA TA SAKI KUNAMAR, JIKAKE TATSATSATSA, ƘARA SAITA WINDOW TAYI TA KUMA HARBAWA, NAMMA SAI RATSARATSA, kan ace me kowa ya mike tsaye yana raba ido. Dawo da bindigar tayi saitinsu tace "yanzu kun yarda na iya harbin ko saina harbe ɗaya daga cikinku?" Shiru kowa yayi yana tsoron kada ta saita shi, "dukanku ku fita ku bani guri" Sifsif kowa ya wuce harda masu rugawa da gudu. Binsu tayi har bakin kofa tare da cewa sauran mutanen "kowa ya kama gabanshi mijina be mutu ba" janyo Kofar falourn tayi ta rufe. Ciki ta koma da sauri zuwa wajen Aayaan ɗin, jikinta sai rawa yake yi, jijjigashi ta fara yi tana cewa "Don Allah yaya ka tashi, kada kayi min haka, don Allah karaimaka mana katashi, ka manta cewa kamin alƙawari cewa in jiraka zaka dawo gareni muci gaba da rainan cikinmu! Don Allah ka tashi!!!! Fashewa tayi da kuka, "wallahi idan baka tashiba kaika zasuyi su rufe a cikin kabari, na roke ka daka dubi darajar Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama ka tashi. Duk wannan abin da takeyi a banza, domin Aayaan yananan a sanƙame cikin likkafani, tashi tayi ta koma cikin ɗakin da gudu, wardrobe ta buɗe ta ciro Brown ɗin jallabiya da gajeren wando ta koma gurin Aayaan ɗin, a hankali ta nutsu tanata cire mishi likkafanin, saida ta gama cirewa tabi duk inda aka sa mishi auduga nan ma ta cire, wandon ta fara sa mishi sannan da kyar tasa mishi jallabiyar, kwashe duka likkafanin tayi ta jefasu gefe, fridge ɗin dake faloun tabude ta ciro ruwa me uban sanyi ya riƙa shafa mishi a fuska tama kuka tana rokonshi akan ya tashi, ganin bafa zai tashi ba yasa ta zauna ta zuba wa kyakkyawar Fuskarshi ido, kallon da take yi mishi kallo ne na ƙurillah, tunda take babu wanda ta taɓa yiwa irin wannan kallon. Fashewa tayi da kuka, ganin yadda Aayaan ɗin ya kara kyau da haske sosai, "yanzu wannan jikin za'a saka a cikin rami tsutsa su cinye?, Innalillahi wa'inna alaihi raji'un!!! Ya Allah mun tuba ka yafe mana!!!! Zama tayi ta miƙar da kafarta Sannan ta ɗauki kan Aayaan ɗin ta ɗora a saman cinyarta tana shafa gashin kanshi, a yadda takeji yanzu game da Aayaan ɗin, ta yarda tayi ta zama dashi a haka da ta yarda aje a binne shi. Tanaji anata buga kofa ana bata haƙuri akan ta taimaka ta buɗe kofar ta bada shi a tafi a kaishi duk mutane sun taru. Duƙar da kanta tayi saitin fuskarshi tanata yi mishi magana tana kuka, kamar daga sama taji Aayaan ya turnuƙe da wani Irin tari sai kace zai amayar da kayan cikinshi, aman wani baƙin abune ya biyo baya kamar wanda yasha Ruwan kwata. A cikin dashasshiyar murya taji yana cewa "ya rabb matata da mamata da yayata" komawa yayi ya rufe ido ƙirjinshi yana sama yana ƙasa da sauri da sauri, faɗin halin da Nawaz ta shiga a dai dai wannan lokaci kamar ɓata bakine, donji tayi ta gama dace a duniya, ita ko yanzu ta yarda ta mutu tunda shi be mutu ba. Jijjigashi ta fara yi tana cewa "yaya don girman Allah kada ka kuma mutuwa, ka tashi ka ganni, nice matarka Nawaz!! Wallahi inasonka, kuma daga yau dai abinda kace kanaso shi zanyi.. Aayaan wanda a tunanin shi har Yanzu yana cikin underground ɗin daya shiga ne yaji Muryar Nawaz kamar daga nesa, buɗe idonshi yayi a Hankali, amma be ganin komai, sai da aƙalla yakai minti ɗaya Sannan ya Fara ganin kamar fuskar Nawaz a saman tashi, yunƙurin tashi yayi amma ya ƙasa saboda yadda jikinshi ya galabaita, motsa bakinshi yayi tare da cewa "is it really you? Ko mafarki nakeyi? Cikin kuka me haɗe da dariya Nawaz tace "wallahi nice, nice Nawaz matarka, don Allah kada ka mutu, ka zauna da Ni" Dago da hannunshi yayi da kyar ya shafi fuskarta, jin da gaske ya taɓa ta yaji itace yasa yaji wani irin ƙarfi yazo mishi, yunkuri yayi ya tashi tare da taimakon Nawaz ɗin, jingina shi tayi da jikin kujera sannan ta kafa mishi robar ruwan data dauko ta zuba mishi dazu "sha" Nawaz tace dashi. Saida ya shanye Ruwan tass sannan yace "sweetheart ya akayi na ganni a cikin gidanmu? A iya abinda zan iya tunawa shine na dira underground sai kawai naji hayaki ƙura da ihu ya baibaye ko ina, daga nan kuma ban ƙara sanin komai ba sai na ganni kusa dake. Rungumeshi tayi gam tana cewa "cewa fa akayi ka mutu, har anyi maka wanka ansa maka likkafani za'a je a binneka shine na kori kowa nace baka mutuba, amma da tuni an binne ka. Tabbas ga likkafanin nan ya gani a gefe, chan ɗaya gefen kuma makara ce a ajiye... Kasa magana yayi ganin bindigarsa ajiye a gefe, "waya dauko bindiga ta?" Ɗaukar bindigar Nawaz tayi tare da cewa "nifa yanzu kaf a cikin Duniyar nan idan aka cireka aka cire ummina babu wani abu daya kai muhimmancin bindigarnan a gurina, saboda itace ta taimakeni ta hana a binneka, da yanzu an cuceni, fashewa tayi da kuka ta miƙe da bindigar riƙe a hannunta ta buɗe ƙofar falourn, mutane ta gani cirko cirko, ganin ta fito ga bindiga a hannnunta yasa kowa ya kwasa a guje harda masu yin gware, "ku shigo kuga ya tashi, wallahi da kun tafka babban kuskure, be mutuba. Zuwa lokacin Kowa yana kallon Nawaz ne a matsayin mahaukaciya, kowa watsewa yayi in banda su Ummin ta dasu mummy sai su Aseey da Sarfraz. Haɗuwa sukayi suka tawo gurinta don su kansu baso sukeyi a binne Aayaan ɗin ba, Abinda Nawaz ɗin tayi ba ƙaramin daɗi yayi musu ba. 💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃. *WANNAN RAWAR TA AAYAAN CE* *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *81* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Jiri ne ya kama Nawaz kafin su ƙaraso kusa da ita, baya tayi zata faɗa, amma tana ƙoƙarin tsaida kanta daga faduwar, sai ya zamana kamar tana layi, Aayaann dake jingine da kujera ne ya gane faduwa zatayi amma take ƙoƙarin hana kanta, cikin Rashin kwarin jiki ya tashi da sassarfa ya nufi inda take. Dai dai nan itama Aseey ta lura da abinda zai faru, dagudu ta ƙarasa dai-dai zuwan Aayaan gurin, dai dai lokacin kuma Nawaz ta yanke jiki ta fadi amma kafin takai kasa Aayaan ya tareta da ƙirjinshi. Kowa tsaye yayi yana kallon Aayaan ɗin cike da mamaki, mutumin dake shirye cikin likkafani amma yanzu gashi tsaye har yana iya taimakon wani mai rai. Aseey kam da sauri ta rungumeshi haɗe da Nawaz ɗin, itama Mummy kansu tayi tana kabbara, baffan Aayaan ne yace "ku lura fa! Kunsan ba kwari ne da Ayatullah ɗin ba, balle ita kuma Nawwarah ɗin. Sakin shi sukayi badon suna soba domin gani suke zai bace, suna sakinshi shima yayi baya zai faɗi, kawu da baffa ne suka rike shi gam, harda taimakon Aseey. Kwantar dashi akayi a saman carpet sannan aka cire Nawaz da itama ke sume a ƙirjinshi. "Innalillahi wa'inna alaihi raji'un!!! Mummy tace tana tafa hannu ganin jini yana bin ƙafar Nawaz yana sauka a ƙasa, hankalin kowa saida ya tashi ganin jinin jajir dashi, Ummin Nawaz ɗin tafi kowa shiga tashin hankali saboda yadda tasan tasha wuya sosai akan zubar jini, tayi ɓarin ciki da zubar jini yafi sau biyar.. Ruwa Aseey ta miƙo aka yayyafa musu amma shiru babu wanda ya tashi, sai dai duka suna numfashi, waje Sarfraz yayi cikin ƴan kai gawa yana cewa don Allah waye Doctor a cikinku? Kusan mutum biyar ne suka ɗaga hannu "kuzo muje, don Allah ana buƙatar taimakonku aciki" Bin bayanshi sukayi ahankali suna tunanin kodai Aayaan ɗin be mutu bane da gaske kamar yadda sukaji wasu na faɗa?, hankalinsu ya tashi matuƙa ganin yadda su biyun suka galabaita sosai, da sauri wani daga cikinsu ya rubuta magunguna a takarda ya miƙawa Sarfraz yace "kayi sauri ka Kawo waɗannan magungunan saboda da alamun guba a Tare dasu duka" Jikin SARFRAZ har rawa yake tsabar tashin hankali, tsoro yakeyi kada suga samu kuma suga rashi, be ɗauki mota ba Kawai ya samu wani zaune akan mashin yace mishi "taimaka ka kaini asibiti" "Wai da gaske be mutu ba!" Mutane keta tambayar Sarfraz "Eh be mutu ba ya tashi" Cewar Sarfraz dai dai sanda mutumin yaja mashin ɗin da gudu zuwa hanyar babban titi. Mamaki ne ya kama kowa jin wai Aayaan be mutu ba, wasu har cewa sukeyi ƙaryane, kuma wai baza su tafi ba suna nan sai sunga yadda za'a ƙare. A cikin gidan kuwa an samu an kai su Nawaz da Aayaan cikin ɗaki kan gado, duba Aayaan ɗin sukayi sosai inda suka tabbatar da guba ce ta sarƙafe huhunshi kuma duka jikinshi ya amshi gubar shiyasa har numfashinshi ya ɗauke na wasu awanni donma Allah ne yasa jininshi ya yaƙi gubar amma da bazai tashi ba. Kan Nawaz suka koma suna duba me yasata zubar jini haka, cikin idonta suka bude, sai tafin hannnunta da jijiyar wuyanta. Amma mama itama fa alamun poisoning ne tare da ita, me taci ne? "Ai Kusan kwana uku bata ci abinci ba saboda koda yaushe allurar Barci akeyi mata, amma ana sa mata drip sosai. Cewar mummy cike da tashin hankali. Ɗaya Daga cikin likitocin ne yace "Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, allurar barci akeyi mata ko da yaushe? Kasheta kukaso kuyi kenan? Ga kuma Alamun ciki nan tattare da ita, yanzu haka idan ba ayi wasa ba cikin ya lalace shiyasa ta fara zubar jini. Wata damuwar ce ta kuma kama kowa dake ɗakin, dai dai lokacin SARFRAZ ya shigo riƙe da ƙatuwar leda a hannun shi ta magungunan da akace ya siyo. Basuyi wata wata ba suka ciri allurar kashe guba sukayi wa Aayaan har guda Uku Sannan akayi wa Nawaz guda ɗaya, saboda sunce allurar barci da aka yi tayi mata ce ta zama makwafin guba a cikin jinin ta. Sunyi kokari sosai wajen ganin jinin ya dena zuba, amma abun yaci tura, sai kawai suka ce ayita addu'a. Drip suka ƙara daura musu tare dayi musu wasu alluran a cikin Ruwan, kowa dai zaune yake yana addu'ar Allah yasa duka su tashi, kada kuma Azo ana murna yanzu kuma suyi mutuwar kasko. *Bayan awa biyu.....* Har zuwa Lokacin basu tashi ba, sai dai numfashinsu ya dai dai ta, fita sallah mazan sukayi inda matan kuma suka yi alwala a cikin gida, kowa ka kalla sai dai kaga yana mui-mui da baki Alamun addu'a, Aseey kam tana zaune a gefe ta zuba musu idanu tana jan carbi, sosai take jin wata irin ƙaunar Nawaz tana ratsawa ta cikin jinin jikinta tana shiga cikin zuciyar ta, "tabbas Nawaz Alkhairi ce a cikin rayuwarsu kamar yadda mummy take cewa, yanzu daba don itaba da tuni Aayaan ya zama labari" Ganin Aayaan tayi ya buɗe ido yana yunƙurin tashi, da sauri ta ƙarasa kusa dashi tare da taimaka mishi yana jingina da jikin fuskar king size royal bed ɗin, "ina sweetheart?" Abinda Aayaann yacewa Aseey kenan Nuna gefenshi tayi da ɗan yatsanta manuniya tace "gata tana barci" Zuba mata ido yayi yana kallonta cike da ƙauna, ga wani uban tausayinta dake ratsa mishi ruhi, dai dai lokacin su baffa dasu kawu dasu daddyn sarfraz, da Sarfraz ɗin kanshi suka dawo daga masallaci,. "kowa saida yayiwa ubangiji hamdala ganin Aayaan zaune har yana magana, sukam dai sunga Ayar Allah, baffa ma be iya yin shiru ba Saida yace "Ayatullah lallai kaci sunan naka *Ayar Allah* tunda gashi ka ajiye mana Aya mun gani da idonmu" Duk da halin da suke ciki saida kowa ya dara harda shi uwar gayyar *Aayaan*, Tea me ɗumi Aseey ta haɗo mishi ta zauna tana bashi a hankali, shan tea ɗin yakeyi amma hankalinshi yana kan Nawaz, kusan minti Talatin da tashin shi amma ita bata tashi ba. Sosai jikin Aayaann yayi kyau don har bayi ya shiga yayi wanka ya canza kaya harda fesa turare, gefen Nawaz ɗin yazo ya zauna, bayan ya duba mata nata drip ɗin, dayake shi tun tuni ya cire nashi. Darduma yasa Aseey ta shimfida mishi ya zauna ya fara jero sallolin da ake binshi a zaune, yana ƙara yiwa Allah godiya da yasa numfashin shi be ƙare ba. Saida a ƙalla yayi Sallah ta yini guda Sannan ya tsaya ya huta, dai dai lokacin suma su baffa suka fita don yin sallar isha'i, mutane kamar mayu har lokacin akwai Wasu zaune a waje basu tafi ba, wadanda suke na jiki kuwa duk Sarfraz ya buɗe musu ɗakin baƙi suna ciki. SARFRAZ ne ya gaji Aayaan ɗin a Yau, domin tuntuni yayi order ɗin abinci a restaurant dai dai yadda zai isa kowa. Har zuwa wannan lokacin kowa mamakin wannan abin sukeyi, akwai ma masu tarar Sarfraz ɗin suna ce mishi wai anya da gaske kuwa ya tashi, kodai basaso a binne shi ne? Murmushi kawai Sarfraz ɗin yakeji tare da cewa "Allah ya kaimu gobe, zaku gani da idon ku" Saida Aayaan yayi sallar yini uku kamar yadda Aseey ta lissafa mishi Sannan ya fara jero ta yau. "La'ilaha'illallahu Muhammad Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam" Nawaz tace tana jujjuya kanta hagu da dama. Sallame sallar Aayaan yayi ya haye saman gadon kamar walƙiya, har Gware suka kusa yi da Aseey, tallabo kanta Aayaan yayi ya riƙe a hannun shi. Wata iriyar zabura tayi tare da cewa "wayyo mijina be mutuba, kada ku binne shi" "Calm down! Calm down!! Gani basu binne niba, ina Tare dake.... A hankali Nawaz ke buɗe ido har ta gama buɗe shi tas a fuskar Aayaan "yaya baka mutu ba Koh" Murmushi yayi mata tare da cewa"in'sha Allah ina tare dake" sunbatar ta yayi a goshi tare da cire mata allurar dake hannunta Sannan ya rungumeta a cikin faffaɗan ƙirjinshi. Jinta takeyi very safe, wani sanyi da daɗi ke ratsa wa ko ina a jikinta. Sam Nawaz ta shafe idonta da toka babu wata kunya, "sweetheart don Allah kada ka kuma zuwa yaƙi" For the first time da ta taɓa kiranshi da wani suna daya danganci soyayyah kenan, farin ciki gurin Aayaan bazai misaltuba, koda kowa ya shigo ɗakin bata sakeshiba shima be sake taba sannan suma basu damu da hakan ba duba da irin haukar da Nawaz tayi musu, sanda akace Aayaan ɗin ya mutu. "Aseey kuje ki taimaka wa Nawaz tayi wanka donta kuma samun kwarin jikinta kafin doctor su dawo" mummy tace tana kallon Aseey ɗin "No mum! Fisbilillah Ina zaune saiki wani ce Aunty Aseey, Ni zan yi mata da kaina Gaskiya " Be jira me mumy zatace ba ya miƙe rungume da Nawaz ɗin a ƙirjinshi ya shiga bayi, kunya ce ta kama kowa dake gurin, waisu wace irin makauniyar soyayyah sukewa junansu da basa jin kunyar kowane, aikam kafin su fito daga bayin kowa ya gudu ya bar musu ɗakin. Tun sanda Aayaan ya fara cire mata kaya yaji zuciyarshi ta tsinke ganin pad cike da jini a jikin Nawaz, ita dakeda ciki meya haɗa ta da pad? Ɓari tayi kenan? Tsoro ne ya kamashi sosai, ya ƙwallafa rai a cikin nan bazaiso ya zube a banza ba, yanaso yaga gudan jininshi wanda yake ɗauke da Babban Tarihi, a ranar daya fara sanin mace a ranar Allah ya assasashi. Sauri sauri yayi mata wankan Sannan ya rufeta da Babban towel ya daukota zuwa kan gado, kayanta ya buɗe ya ciro doguwar riga yasa mata mara nauyi, so yake yaje asibiti yayi mata scanning donya tabbatar da abinda ke faruwa. Allah yasa muji Alkhairi..... *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *82* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Cikin sauri sauri ya gama shirya Nawaz ɗin, ɗaukarta yayi ya tawo falour "yaya ka saukeni kaga ba lafiya ce dakai ba" cewar Nawaz Saboda sosai take tausaya mishi idan ta tuna har likkafani ansa mishi. "Komai zan iya yi akanki, kuma daga yau kada ki kuma yi min magana Idan na ɗaukeki Saboda Ni sam bana jin nauyin ki" Gum Nawaz tayi da bakinta saboda yanzu sam bataso tayi mishi Abinda zaiji babu daɗi. Kallon duka Mutanen dake zaune a Babban falourn yayi yace "zamuje asibiti zanyi mata hoto inga cikin yana nan ko ya zube" Kowa kallon wannan ƙarfin halin yakeyi, mutumin da Yan awannin baya yake kwance be iya motsa koda yatsanshi ne yanzu yake tsaye dauke da mutum, lallai Allah shine mai iko akan komai da kowa, Mummy ce tace "haba Aayaan! Dukanku fa ba lafiya ce daku ba, don Allah kabar yarinyarnan ta huta gobe sai kuje" Ganin Idan ya tsaya sanya mummy zata hanashi sai kawai yace "mummy Don Allah Don darajar Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam kibarmu muje" Baffa ne yace"kibarshi yaje amma ɗan uwanshi Sarfraz ya kaisu a mota" Ummin Nawaz kam kunya ta isheta, wannan abu nasu Nawaz yana bata mamaki, wai har yaushe suka shaƙu da juna haka? Yankewa tayi gobe in'sha Allah zata tafi gida tunda dai Allah yasa be mutu ba, da ace ya mutu ne to dole ko kwana bakwai tayi zuwa a share makoki. Fita SARFRAZ yayi da sauri don yayi warming ɗin motar kafin Aayaan ya ƙaraso, dayake dole sai anbi ta usulin main falour za'a fita daga gidan yasa mutane suka riƙa tsaida Aayaan, jaje kowa keyi mishi inda wasu kuma suke tambayar meya faru da Nawaz ɗin.. Sarfraz ne ya koma cikin gidan Don ganin me ya tsayar da Aayaan ɗin ya hanashi fitowa har zuwa lokacin, a main falour sukayi kicibis da Aayaan ɗin wanda ke tsaye rungume da Nawaz a hannunshi. Ran Sarfraz a bace ya hau cewa "Don Allah ku bari mu dawo saiku yi mishi duka tambayoyin da kukeso kuyi mai, yanzu sauri mukeyi zamu kai mara lafiya asibiti kuma dare yayi" "Muje yaya" cewar sarfraz yana dafa kafaɗar Aayaan ɗin Koda suka shiga motar Aayaan be sauke Nawaz ba illa gyara mata zama da yayi a Saman cinyarshi, "wai yaya meyasa kacika sanyi ne? Kasan abinda ya fito damu amma ka tsaya biyewa mata suna Daɗa ɓata maka lokaci. "Bro banason Mutum yaga kamar na wulakanta shi ne, sam banjin daɗi naga wani ya shiga cikin damuwa komi kankantarta balle kuma ace nine sila. Haka dai suka isa cikin harabar Asibitin, Parking Sarfraz yayi sannan ya fito ya buɗewa Aayaan ƙofar motar, yana kallo Aayaan ya shiga cikin hanyar da zata sada ka da ko wane ward kakeson zuwa, tsalle yayi ya zauna a saman motar yana kalon cikin Asibitin. Da kalle kallen ya ishe shi sai ya ciro wayarshi ya bude wajen video, mutanene maƙil tsaye a ƙofar gidansu Aayaan, wasu ma kuka sukeyi wasu kuma idonsu yayi jajir alamun sunma gaji da kukan, "wai me yaya Aayaann yake yiwa Allah ne da ya zama mai wannan uban farin jinin? Mtsewwwss! Kodai kulawar da taimakon da yakeyiwa al'ummar Annabi ne? Girgiza kai yayi sannan yace "tabbas hakane, domin daba don shiba da yanzu Allah ne kadai yasan yadda rayuwata zata kasance, ko na haukace ko kuma ina cikin dajin su hassu inata shirme, murmushi ne ya kufce mishi daya tuna da hassu, sam ya manta da babinta tunda suka iso garin, sai yanzu da zance yazo kanta. Aayaan yana shiga be tsaya a ko'ina ba sai a ultrasound Room, a mutunce cikin girmama wa docton dake ciki ya gaida Aayaan Sannan ya tashi daga seat ɗin dayake zaune, saida ya kwantar da Nawaz a saman gadon scanning ɗin Sannan ya zauna a seat ɗin tare da cewa likitan wanda ke tsaye yana jiran umarni "you can go" juyawa yayi ya fita daga ɗakin. Saida ya saita komai Sannan ya ɗaga rigar Nawaz saboda shafa mata ultrasound gel, cikinta wanda ke shafe ya kalla yanajin wata yar fargaba na kamashi. Saida aƙalla yakai kusan awa ɗaya yana abu ɗaya, idonshi duk yayi ja ga wata zufa data ke tsatstsafo mishi a goshi. Kuka yakeson yayi ko kila ya samu sauƙi daga Abinda yakeji, amma kuma zuciyarshi ta ƙi bashi haɗin Kai, buga tebur yayi yana cewa "wane mara hankalin likita suka kira wanda ya riƙa dirkawa matata allurar barci kamar wata mara galihu? Gashi yanzu ya jamin asara mafi girma a duniya" cije lebenshi yayi yai ƙwafa sannan yace "gaskiya saina ɗauki tsatsauran mataki akan koma wane likita ne, fisbilillah yanzu da hantarta ko ƙodarta ta samu matsala fa?" A hankali Nawaz ta sauko daga saman gadon, takowa tayi har zuwa gabanshi, zama tayi saman cinyarshi tare da rungumeshi sosai. "My Reality ban sanka da saurin fushi ba, kuma ban sanka da rashin haƙuri ba, Ni nasanka da yarda da ƙaddara, da hakuri da kawaici!!! Don Allah kada ka sauya daga yadda na sanka wato kyakkyawa kuma mai kyakkyawar zuciya. Idanma Allah yasa cikin ya zube to please inaso ka ɗauka jarrabaka Allah yakeso yayi, to kayi hakuri ka ɗauki kaddara sai Allah ya chanza maka da mafi alkhairi a garemu baki ɗaya, kuma banso ka manta cewa da ba don ƙudirar Allah ba da yanzuma ka manta da wata rayuwa wai ita *Rayuwar Duniya*, to da me kenan yanzu? Kuma idan yara kakeso Ni nayi maka alƙawarin zanta haifa maka su har saika ce nabarshi haka" Kallonta kawai Aayaan yakeyi yana mamakin Irin basirar maganar da Allah ya bata, Lallai shiyasa Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yace "Duniya wajen ɗan jin daɗi ce amma mafi alkhairin jin daɗin duniya shine mace tagari" Lallai yau yagani da idonshi, Domin Kafin ta iso gareshi ji yake Kamar zuciyarshi zata fashe amma zuwan ta da kalamanta masu sanyi sunsa yaji komai ya goge daga cikin zuciyarshi. Fuskarta ya ɗago yana kallonta "kince kinyi alkawarin haifa min yara da yawa, to da wannan tsoron naki zaki haihu ɗin?" "I promise!! Kuma ka bari jinin ya dena zuba zakasha mamaki" "Wai meya chanza Nawaz haka lokaci ɗaya? Shifa abin har tsoro yake bashi, zallar kaunarshi yake gani a cikin kwayar idonta kuma sam yanzu babu wannan kunyar dake Kawo mishi cikas" Shima daɗa rungumeta yayi sosai yana ajiyar zuciya a hankali, "dear mutafi pharmacy in sai miki magunguna sai mu wuce gida Koh? But me zaki ci?" Shagwaɓe fuska Nawaz tayi sannan cikin yanga da jan aji me cike da salo tace "kaza da madara da ice cream" Dariya ce ta kwacewa Aayaan "Allah Sarki little Aayaan, yazo ya koya miki kwadayi shi kuma ya tafi, aini ko duka kajin duniya kikeso ki cinye in'sha Allah sai an nemo Miki su" Murmushi Nawaz tayi sannan cikin salo da salsala tace "godiya nake yi ranka ya daɗe, Allah ya ja kwana yasa sai kaga jikokin yaranka ma, kuma bi'iznillah tsufa me cike da lafiya zakayi" "A'a wai me ya kawo wannan chanjin ne lokaci ɗaya" Abinda Aayaann ya tambayi zuciyar shi kenan cikin ƴan sakwanni. "Wallahi da ace ka mutu da gaske ko! To wallahi haukacewa zanyi babu ko tantama, nifa a Lokacin gani nakeyi kamar ni kadai ce a cikin Duniyar nan, Don Allah habibi kada ka kuma zuwa yaƙi" Nawaz fa Neman rikita Aayaan takeyi, ba lafiya gareshi ba amma duk ta dagula mishi lissafi, "wai Nawaz dai daya sani ce wannan?" Ita kanta Nawaz bawai da gangan take yi mishi abubuwan da take yi ba, ita kanta Batasan ma tanayi ba, tsabar tsagwaron kaunarshi ce kawai take fito da kanka da kanta, tunda dama ai bahaushe yace *SO BAYA ƁUYA* . "My soulmate bakace komai ba!" Nawaz ta faɗa kamar zata zunduma ihu. "I'm sorry sweetheart, bazan kuma zuwa ba" Kanta ta ƙara cusawa cikin ƙirjinshi tana sauke ajiyar zuciya a Hankali "Yaya na rasa wane irin so nakeyi maka, yanzu haka ji nakeyi kamar in shige jikinka mu haɗe mu zama ɗaya" Lallai akace mahakurci mawadaci, kuma lallai addu'a bata taɓa faɗuwa a ƙasa, wai yau shi Aayaan Nawaz ke faɗawa duka wadannan maganganun, shikam ina zaisa kanshi don farinciki, dama ace yau ƙalau take da saiya nuna mata irin tashi tsantsar ƙaunar da yake yi mata. But never the less yasan kwana nawa ne jinin ze dauke" "MADINATUL MUNAWWARAH! Na ƙaunace ki a cikin rayuwata, na soki son da ban taɓa zaton zan iya yiwa kowa ba, bani da burin daya wuce naganki kina cikin farin ciki, kyau kikeyi sosai idan kina cikin farin ciki da murna, bazan miki ƙarya ba amma wallahi ko sanda naji numfashina yana ɗaukewa babu wanda ya fara faɗo min a cikin zuciyata face ke" "Ina ƙaunarki, ƙaunar da bansan irin taba, Don Allah kada ki gujeni koda wasa, plssss sweetheart mu rayu cikin so, kauna da aminta da juna, pls ko laifi nayi Miki ki faɗa min wallahi zan baki hakuri, amma kada kice zaki hukunta Ni da fushinki. Nan suka taɓarɓaren, kowa yana faɗawa ɗan uwanshi irin kaunar da yake yi mishi.. Ganin sha ɗaya tana nema wucewa yasa Aayaan kashe duka na'urar scanning din, ɗaukar Nawaz yayi ya tallabeta tare da miƙewa Sannan suka fita zuwa doguwar hanyar dake ɗauke da kowane daki a cikin asibitin, tsirarun mutanen da suke waje ne sukayi ta gaishe shi tare da natsuwa kada suyi wani laifin, wasu kuma mamaki neman kashe su yayi saboda sunji labarin ance ya mutu. Koda ya ƙarasa gaban motar, cewa SARFRAZ yayi "Don Allah bro I'm sorry, na barka kai kadai ko?" Murmushi SARFRAZ yayi "wallahi a'a Ni naga ma saurin fitowar ka, zaune nake inata amsa waya anata tambayata wai baka mutu ba ko?" "Oh wai haka abin yabi duniya" Aayaan yace yana shiga cikin motar. "Wallahi yaya, ai farin jini gareka na fitar hankali, kaga yadda mutane suka taru kuwa? Wasu kuka kawai sukeyi kamar suma zasu mutu. Murmushi Nawaz tayi tana ƙara lafewa a cikin jikinshi, ji take yi kamar ta dauwama a haka. Koda suka fita daga Asibitin a wani babban pharmacy suka tsaya Aayaan ya amsar mata magunguna sannan suka biya ta Almas ya amsar mata duka Abinda tace tanaso harda ƙarin wadanda ma bata ce ba. SARFRAZ dai kasa shiru yayi "wai yaya naga baka fito da kuɗi ba amma duk inda kaje sai inga sun baka abu cikin rawar jiki da girmama wa" Murmushi Aayaan yayi yace "talk active" "Yaya don Allah ka faɗa min meye sirrin" cewar sarfraz yana kama hannun Aayann. "Okay to ɗan jarida, duk inda kaga munje yanzu mallakina ne?" Zaro ido Sarfraz yayi "wai yaya kana nufin asibitin da pharmacy ɗin da Almas ɗin duka nakane?" "No more questions, eh duka nake nufi" Jinjina kai kawai SARFRAZ yake yi yana jinshi kamar a saman iska, lallai shi ɗan gata ne, ace wanshi ne keda duka wannan abubuwan, ai wallahi sai yayi dinner na murnar be mutu ba, yanzu daya mutu shikenan. Suna shiga gida sukayi kicibis da colonel zaune a Babban falour tare da mummyn Sarfraz da mummyn Aayaan da Ummin Nawaz dasu baffa harda Daddy shima. Da sauri colonel ya miƙe "Allah Nagode maka, Allah nayi maka alƙawarin gobe zan yanka raƙuma guda goma nayi sadaka da naman" A saman kujera Aayaan ya kwantar da Nawaz Sannan ya ƙarasa gaban Colonel suka rungume juna, fashewa da kuka colonel yayi "my son da ace ka mutu bansan ya zanyi ba, ina sane fa naki zuwa gidan nan jana'iza, saboda bazan iya jure ina kallo a saka a cikin kabari a binneka ba, yanzu haka su Naufal da Fudail ne suka koma suka cemin wai ance ka tashi baka mutuba, amma dai basu ganka ba, shiyasa fa na iya zuwa." "I'm sorry daddy, haka Allah ya tsara sai muyi tayi mishi godiya tunda da sauran numfashi " "Kowa mamakin irin shakuwar colonel da Aayaan yakeyi, amma Mummy batayiba saboda tasan Yadda colonel ɗin suke da daddyn Aayaan kafin ya rasu.. Zaune kawai Colonel yake amma hankalinshi na kan mummy, ya rasa meyasa har yanzu ta ƙi amsar shi a matsayin mijin aure, yayi mata hannunka me sanda har ya gaji ya fito fili ya faɗa mata amma tace ita bazata iya aurenshi ba tana Matsayin ƙawar matarshi ba. *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *83* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Tsaff mummy na ankare da kallon da colonel yakeyi mata, tasan jimawa da sukayi basu haɗu bane shiyasa daya ganta yanzu ya kasa kauda kanshi a kanta. "Ai ko mutuwa zakayi saidai kayi, babu yadda za'ayi in aureka bayan Ni ƙawar matar kace, aima cin amana kenan!" Cewar mummy cikin zuciyarta tare da jin takura da kallon da colonel ɗin keyi mata Duƙawa Aayaan yayi ya ɗauki Nawaz da ledar kayan ciye-ciyen ta, "Son ai daka barta anan ɗin tunda barci takeyi" Sarai Aayaan yasan ba barci takeyi ba, yasan kunya ce tasa ta kasa buɗe idonta, "No Mummy bari kawai na kaita ɗaki saboda nan kinga akwai hayaniya da yawa" "Okay to cikin yana nan kuwa?" Cewar mummy tana kallon move ɗin Aayaan ɗin, yadda taga ya kaɗa kai ya juya a raunane yasa ta gane cewa babu cikin tunda tafi kowa sanin halin ɗan nata. Zuciyarta kamar zata fashe, taso ace an haifi cikin, to Amma tunda Allah yasa shi Aayaan ɗin be mutu ba ai hakan ma ya wadatar, tasan cikin ɗan ƙanƙanin lokaci za'a kuma samun wani cikin duba da yadda suke kwakwumewa juna. *Aayaan....* Yana shiga ɗakin ya ɗora ta a saman gado "Sweetheart tashi kici Abincin" zaune Nawaz ta tashi tana murmushi "Yaya wai meyasa kowa sonka yakeyi? Farin jininka yayi yawa Gaskiya, amma kuma a hakan ne ka zauna har zuwa yanzu bakayi Aure ba?" Rungumeta a cikin ƙirjinshi yayi Sannan yace "eh mana! Dole naƙi yin Aure tunda ina jiran my Sweetheart" Daɗi sosai taji maganar tayi Mata, ita ba mace bace mai son a riƙa yaba mata ba, amma kuma duk sanda Aayaan zai yabeta saita ji ta kamar ta tashi sama tayi shawagi tsabar murna. "My soulmate I so much love you, wallahi har yanzu zuciya bata dawo dai dai ba, na rigada na shiga damuwar da ban taɓa shigan taba." "Nafiki sonki, shiyasa Allah yasa na dawo, amma kuma mun rasa little Aayaan" "Hmmm Allah ne kawai ya dubeni da idon rahama yasa baka mutu ba, amma da Yanzu nabi titi" "Dear ki dena wannan maganar, in'sha Allah muna tare har abada, yanzu dai ƙoƙarta ki samu kici Abincin kada yunwa ta illata min ke" Murmushi Nawaz tayi tare da miƙewa tana yin hanyar bayi don ta wanke baki, bata Ankara ba tajita a sama cikin iska "dear ina kusa amma sai kiyi ta wahalar da kanki" Aayaan yace yana direta a gaban sink, toothpaste yasa mata a brush sannan yace "open Your mouth" A hankali Nawaz ta buɗe bakin saboda taso ne ace ya barta tayi da kanta. Sosai jerarrun fararen haƙoranta suka birgeshi, tsaff dasu gwanin sha'awa, sosai siriyar hushiryar dake tsakanin haƙoran ta ƙara ƙawata su. Tsaff ya wanke mata bakin ya ɗauraye, kuma daukota yayi ya dire a tsakiyar gado Sannan ya buɗe mata madarar ya miƙa mata "fara shan wannan saboda hanjinki ya warware, amsa tayi tasa a bakinta, saida tasha kusan rabi Sannan ta fara cin naman kazar.. Bata wani ci da yawa ba tace ya isheta, "to yanzu babu ke babu yin Barci sai anjima tunda kinga bakici abinci da wuri ba, bazai yiwu ki kwanta ba saiya faɗa Miki" "Wallahi yaya barci nakeji sosai " cewar Nawaz tana kwanciya a saman cinyarshi "Oya tashi ki zauna! Ko kinaso kiyi ƙaton ciki ne? Ɗagota yayi ya zaunar da ita. Laptop 💻 ɗinshi dake gefen side drawer ya janyo, buɗe ta yayi ya kunna yana ɗan danne danne, be lura ba ashe har Nawaz tayi barci a zaune, Murmushi yayi ya gyara mata kwanciya, shafar fuskarta yayi yace "sleeping beauty kawai!!" Tsayawa yayi da danne-dannen system ɗin, tunawa yayi da CCTV carema a cikin babban falour, sosai yaji yanaso yaga abinda ya faru sanda akace ya mutu. Be jira komai ba ya janyo wayar ya jona sannan ya kunna media ɗin, duba date ya farayi yana wucewa har Saida ya iso date ɗin yau sannan ya tsayar, Bega kowa ba illah tsirarun mutane da suketa shiga suna fita, forwarding yayi Sannan ya tsayar da sauri ganin an shigo da akwatin gawa, hankalin kowa a tashe, wasu ma kuka sukeyi bilhaƙƙi. Sosai ya maida hankali yana kallon cikin laptop ɗin, shine kwance cikin akwatin baya ko motsi, tasbihi ya riƙa yiwa Allah tunda ya fara kallon har zuwa inda aka fara yi mishi wankan gawa, wani irin tsoron Allah ne yaji yana ƙara shigar mishi zuciya "lallai mutuwa wa'azi ce babba. Sanda aka fara sa mishi likkafani Saida yayi kuka "lallai mutum ba a bakin komai yakeba, shine kwance sai yadda aka juyashi?" Tsoron Allah ne wanda be taɓa jin irinshiba ya dirar mishi a cikin zuciyar shi... Yana kallon kowa ta cikin laptop ɗin, addu'a suke tayi mishi , masu kuka ma suna tayi, Tunani ya fara akan ina Nawaz, saboda tunda ya fara kallo be ganta ba ko sau ɗaya ba, kafin ya fara ba kanshi amsa sai ganinta yayi ta fito tana layi. Tana tsaye sai kuma ta koma, fitowar da zata kumayi shine ta fito riƙe da bindiga tana nuna musu, tundaga fasa TV da tayi har zuwa sanda ta kori kowa ta dawo tana jijjigashi zuwa chanza mishi kaya, maganganun da takeyi da kukan datakeyi duk babu abinda be gani ba, "Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un?" Mutun ba'a bakin komai yakeba... Fuskarshi yakai saitin fuskar Nawaz ya zuba mata Ido, "yaushe Nawaz ta fara sonshi haka? Shikam me zeyi yaji daɗi a cikin ranshi? Farin cikin da yake ciki ya kasa barin zuciyarshi ta huta, lallai Allah maji rikon bawa ne, tunda yake be taɓa kawo cewa Nawaz zata iya yin quarter ɗin Abinda tayi ba, lallai dole ayi mata alluran barci, ɗagota yayi ya haɗa da ƙirjinshi ya matseta wai ko zai samu relief, amma inaa wani irin maganaɗisun ƙaunarta ne da sonta ke ƙara shatata a cikin zuciya, ruhi da gangar jikinsa, jiyakeyi kamar numfashinshi zai ɗauke. A Yanzu kam Aayaan gani yakeyi shima idan babu Nawaz bazai iya Zaman duniya ba, a yadda yakeji a ranshi ma gani yakeyi numfashin ma da yake shaƙa Nawaz ce ta nemar mishi alfarma, yasan mata da mugun tsoron gawa amma ita sam bataji tsoron Shiba, saima dakumarshi data riƙa yi tana rungumar shi. "Shikam me zaiyi wa Nawaz ya biyata, ya tabbata da badon Allah yaba Nawaz ikon yin hakan ba da tuni yana cikin Rami ya fara kumbura. Kwantar da ita yayi cikeda kulawa kamar kwai, sannan ya tashi ya shiga bathroom ya ɗauro Alwala, nafila ya riƙa jerowa yana yiwa Allah godiya da kirari Sannan yana ƙara yiwa Nawaz addu'oin gamawa da iyaye da duniya lafiya, a yadda yakeji da shine me mukullin Aljannah da kyauta zai bata kawai yace ta shiga ta huta. Sai tsakiyar dare Sannan ya dena yin sallar ya nufi gado ya kwanta, janyota yayi saman ƙirjinshi yanajin zuciyar shi kamar zata faso ta fito waje, lallai Nawaz ɗaya ce Tamkar da dubu, wato sosai ta iya harbi amma sai tayi tamai alayen cewa bata iyaba. Koda asbah tayi shi ya fara tashi, rasa Yadda zai tashi Nawaz ɗin yayi domin a yadda yakeji yanzu game da ita bazai iya ɓata mata raiba, abinci ma da ana taunawa mutum to da tauna mata zaiyi ya haɗiye sai dai ya shiga cikinta direct (```Nikam Matar Rasheed nace dama ya lafiyar kura balle yanzu```) Haɗe bakinsu yayi guri ɗaya yana bata French kiss, mutsu mutsu ta fara tare da buɗe idonta ahankali, tsaff ta sauke su a kan fuskar Aayaan da yake yi mata wani irin ƙayataccen murmushi wanda ke ɗauke da faassarori daban daban, "sweetheart I'm sorry! Natasheki Koh?" Murmushi itama Nawaz ɗin tayi ba tare data ce komai ba. "Lokacin Sallah ne yayi shine nace bari na tasheki" "Ka manta bana Sallah" Kamar saukar Aradu haka yaji maganar Nawaz "Don Allah kiyi hakuri wallahi na manta ne" duk sai yayi fuskar tausayi Tashi zaune Nawaz tayi tana dariya mara sauti "my reality ji yadda ka tada hankalinka kawai don ka tashe ni daga barci! Ni daɗi naji sosai sanda nayi ido huɗu da kyakkyawar fuskarka, wallahi yaya baka san irin kaunarka da Allah ya dasa a cikin ruhina bane, ina kaunar ka kamar na mutu" Tausayi sosai taba Aayaan domin yagani da idonshi, yasan ƙaunar da take yi mishi pure ce babu algus a cikin ta Rungumeta yayi yana patting ɗin bayanta a hankali, Sannan ya Fara magana kamar haka "matata basai kin zauna kina bata bakinki Wajen faɗa min Irin ƙaunar da kike yi mini ba, Ni na gani kuma naji sannan na amince, kuma nayi miki alkawarin cewa indai nine hanyar zuwanki Aljannah to na yafe duniya da lahira, ki shiga Aljannah salin alin" "Nagode sosai sweetheart Allah ya ƙara girma" Nawaz tace tanajin wani irin shauƙin mijin nata yana fusgarta. Kwantar da ita yayi sannan yace "Sleep, Ni zan fita Masallaci Amma i will be back soon" "Allah ya dawomin dakai lafiya habibi" Fita Aayaan yayi yana jin cewa Nawaz so kawai takeyi ta haukatashi, Koda ya fita zuwa masallaci haka mutane sukayi tayi mai Allah ya kyauta ya kuma kiyaye gaba, harda masu cewa ashe dama matarshi soja ce itama, wai an basu Labarin abinda ya faru, shidai as usual haka yaita yi musu murmushi, da yake babu waya a hannunshi tana cikin kaya shiyasa mutane sukayi mishi yawa a Masallacin, sai wajen ƙarfe shida da rabi ya samu ya gudo zuwa gida. A falour yaci karo da mummy "ina kwana mummy?" "Lafiya Lau son! Ya ka tashi?" "Nima lafiya Lau Alhamdullillah" "Masha Allah, yanzu ina daughter na take?" "Tana barci" Aayaan yace da ƴar Alamun kunya kadan a Tare dashi "To yanzu ya za'ayi da shirye-shiryen komawar mutane gida?, Kaga duk don kai sukazo, kuma ya kamata ka haɗa wa kowa sha tara na Alkhairi Saboda mai sonkaene kawai zaizo inda kake a lokacin da ka zama gawa." Kafin Aayaan ya bada amsa saiga Colonel ya fito daga ɗakin da ya sauka riƙe da madaidaiciyar jaka , mummyn Aayaan ya gaisar dayake sun gaisa da Aayaan tun a masallaci "Na shirya zan tafi, son Allah ya ƙara sauƙi ya kiyaye gaba, sai yaushe kuma zamu haɗu?" Murmushi Aayaan yayi tare da cewa "sir ai ko gobe kake son ganina i am ready to come" "Nop bazan ma so ganin kaba, yanzu dai ka tsaya ka ƙara samun kwarin jiki sannan ka kulamin da daughter na sosai." Har Cikin mota Aayaan ya rakashi, sosai ya lura Akwai magana a bakin Colonel Amma yaƙi yi, ganin be faɗa ba sai kawai ya basar shima ya koma gida. Koda ya koma cikin ɗaki tarar da Nawaz yayi tanata sharar barcinta hani'an, murmushi yayi tare da sunbatar ta a goshi Sannan ya gyara mata kwanciya, kuma fita yayi domin ya samu ya gama haɗa komai da yakeso ya haɗawa yan Zaria tunda sune waɗanda zasu fara tafiya. Fam ya cika musu Boot da kayan masarufi, Sannan yaba security Dinshi dubu ɗari ɗari yace idan sun sauke kowa ya basu, dakyar aka samu Sarfraz ya yarda cewa zai koma, amma da fir yaƙi, dama masu komawa zaria ɗin, mummyn sarfraz ce da daddy sai ummin Nawaz da Sarfraz ɗin kanshi, sai kuma wata innar hassu. Tuni gida ya fara komawa NORMAL saboda waɗanda ke nan cikin Maidugurin duk sun tafi, kamar su baffa da sauran yan gidansu kakannin Nawaz, da waɗanda suka samu zuwa daga gidan surukan Aseey dama kakannin shi Aayaan ɗin kanshi.. Bashi ya samu sukuni ba sai wajen ƙarfe goma, koda ya koma cikin ɗakin barci ya tarar Nawaz nata sharɓa, a gefen side drawer kuma ga vacuum Flask da warmer Alamun an kawo mata break fast. "Wai ko dai har yanzu allurorin data sha basu gama sakin taba ne?, Tun jiya da dare fa take barci" Daƙyar ya tasheta ya bata Abincin Sannan sukayi wanka, laptop ya kunna yana nuna mata wasu sabbabin site da yakeso ta zaɓi wanda take so, ji yayi yanata magana amma shiru babu Amsa, waigawar da yayi sai ganin Nawaz yayi tanata kwasar barci abinta. Girgiza Kai yayi yai murmushi sannan ya kashe laptop ɗin, gyara mata kwanciya yayi Sannan ya fita zuwa falour. Anan yaga muhsin wanda gaba ɗaya ya manta dashi, da gudu ya tawo ya faɗa kanshi yana dariya "Uncle yanzu uncle saddam ya dawo dani daga gidansu gwoggo (surukan Aseey) yace ma wai yanata kiran wayar ka bata shiga, kuma wai in gaishe ka. "Ina ansawa dear, zakasha chocolate?" Aseey ce tace "Babu wani chocolate da zaisha Don Nima inaso na zauna da dan uwana mu tattauna, da yanzu Shikenan bazan Kuma ganinkaba da Nawaz bata hana a kaika ba, gaskiya bro Nawaz mutum ce, kuma Rahma ma ce a tattare dakai da muma baki ɗaya, wai kam kaga yadda ta fiyace ranar da aka sanar cewa an saka muku bomb?" Haka Aseey ta zauna ta zayyanewa Aayaan komai da Nawaz tayi. Shi dai shiru yayi yana ƙara yiwa Allah tasbihi a Cikin zuciyarshi Mummy ce ta fito da sauri kamar zata tashi sama, fuskarta cike da tashin hankali "Aseey je kira Aayaan" ta faɗa ba tare data lura da Aayaan dake zaune cikin sofa ba "Mum gani nan" cewar Aayaan da alamar damuwa shima tattare dashi, saboda yadda yaga Mummyn nashi cikin tashin hankali "Yauwa Aayaan! Yanzu na gama waya da Naufal wai mummyn su ta Rasuu" A zabure Aayaan ya miƙe tsaye cikin tashin hankali saboda zuwa yanzu yasan meye mutuwa "mummy shi colonel ɗin yana ina?" "Yana gefe shima amma dai bamuyi magana dashiba" mummy ta faɗa cikin kololuwar tashin hankalin da yake nuna taji mutuwar ƙawar Tata. Aseey ma tsaye take ta rungume hannayenta tana tuna irin alkhairin matar a gareta, "mummy wai dama batada Lafiya ne" Aseey ta tambaya cikin jimami "Eh batada lafiya paralyzed ya kamata bayan kin koma England." ALLAH sarki rayuwa, Allah ya jikanta yasa ta huta, wallahi naji mutuwar baiwar Allahn nan, akwaita da haƙuri da kawaici ga mutunta ɗan adam. Shiru Aayaan yayi yana nazari inda daga bisani yace "zuwa Abuja fa ya kama mu yau ɗin nan," Mummy bata hana ba saboda itama tanaso taje gaisuwar ƙawar tata, "kowa ya shirya kafin karfe huɗu Flight ɗin yamma zamu hau" Aayaan yace yana nufar dakinshi. Zare ido yayi ya tsaya yana kallon Nawaz da mamaki ganin ta tana.......... Kwana biyu kun jini shiru ko, Ammin rasuwa ne, ina yiwa kowa Fatan Alkhairi.... Allah ya yafe mana kurakuran mu *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *84* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Zare Ido yayi ya tsaya yana kallon Nawaz da mamakin ganinta tana Sallah, "dear jinin ya tsaya ne?" Sai kuma yayi shiru sanin babu me bashi amsa tunda Sallah takeyi Gefe yaja ya ɗauki medium ɗin luggage ya fara zuba musu kayansu, yawancin na Nawaz duka Abaya ya zaɓar mata, shima dai ba wasu kaya bane na Azo a gani ba. Yana gama shiryawa itama dai-dai lokacin ta idar da Sallar "my soulmate Naga kana haɗa kaya a akwati?" "Dear wallahi zuwa Abuja ne ya kama mu urgently, yanzu mum ta gama waya da Naufal wai mum ɗinsu ta rasu?" Duhu Nawaz ta shiga domin bata gane inda zancenshi ya dosa ba "dear waye Naufal?" "Au na manta baki sansu ba, yaran colonel ne Naufal da Fudail, Amma dama ba wannan data rasun bace ta haifesu, tun suna jinjiraye maman su ta rasu bayan ta haifesu, to shine a garin su aka bashi auren wannan data rasun, Matace mai karamci da mutunci sosai, munsha zuwa gurinta muyi hutu sanda daddyn mu yake raye, ƙawar mummy ce sosai." Rausayar dakai Nawaz tayi, irin Alamun tausayin nan, "Allah sarki, Allah ya jiƙanta yayi mata rahma yasa ta huta, mu kuma Allah ya bamu ikon yin Abinda mukazo duniyar yi" "Ameen dear thanks, yanzu muje muyi wanka saimu shirya saboda su mummy na jiranmu," Tsayawa yayi yana kallonta sai kuma ya kanne ido ɗaya as usual "ko na tsaya na Angonce tukuna? Kinga sai muyi wankan mu me hujja koh" Ita dai Nawaz shiru tayi kanta a ƙasa batace komai ba, shima be kuma cewa komai ɗinba ya sunkuceta zuwa bathroom, "wasa nakeyi miki fa, ai yaci na barki kiɗan huta koda na kwana uku ne, kada naje a kuma yin tuntuɓe da wani cikin a bakin ƙofa" Duk da cewa Nawaz ba wani kunyarshi takeji yanzu ba amma Saida maganar shi tasata rufe ido tana dariya ƙasa-ƙasa. Bayan wasu Yan mintoci har sun shirya abinsu, tsaff sukayi gwanin ban sha'awa, sai tsokanar Nawaz Aayaan yake tayi barin ya lura tanata ɗan kannewa "yasan tsoron haɗuwarsu takeyi domin yasan da tasan zai shigo ya ganta tana Sallah da batayi lokacin ba. Ta ɓangaren Nawaz kuma duk sai take Dan jin fargaba na kamata kaɗan saboda yadda taga yanata nan-nan da ita, gashi dama an daɗe ba'a haɗu ba, kuma tasan Aayaan har dai ya chafke ka saiya ƙureka duka sannan zaice zai fara komai. Tunawa tayi da second night ɗinsu yadda tasha fama, Saida tsigar jikinta ta tashi saboda tunawa da tayi da irin aika-aikar da yayi mata, har kuka tayi wiwi akan ya dena amma ko'a jikinshi (wai an yakushi kakkausa). Ita ba komai ke damunta ba irin yadda yake tasa ta da taɓe-taɓe, taɓa chan taɓa nan, matsa nan, matsa chan, tsotsi nan tsotsi can, duk saiya ƙureta tass taji kamar numfashinta zai ɗauke, dama ace idan yazo Abinda yazo yi zaiyi ya wuce amma ita tasan ta shiga ukunta, duk abinda yasa jikinta yin sanyi kenan, barin dataga duk motsi saiya kashe mata ido tare da ɗaga gira. A falour suka haɗu dasu mum duka don tafiya Airport, mummy na matukar jin daɗin Yadda Aayaan da Nawaz suka fahimci junansu, Aseey ma haka. *Some hours later....* Su mummyn Aayaan ne da Aayaan ɗin da Aseey da Nawaz sai Muhsin, zaune a Babban falourn baƙi na gidan colonel, falourn cike yake da masu Amsar gaisuwa, kowa kagani kasan ba'a cikin kwanciyar hankali yakeba. Mummy ma sosai hankalinta ya tashi ganin da idan suka zo gidan ita marigayiyar suke gani taita hidima dasu. "Lokacin sallar magrib yayi, bari muje masallaci" cewar colonel yana miƙewa tare da dafa kafaɗar Aayaan, ita dai mummy na zaune sanye da hijabi tanata jan chasbaha. Aseey da Nawaz ma haka suna gefe a zaune sunyi jugum-jugum, bayan su Colonel sun fita ne suma suka tashi don gabatar da tasu sallar. Ba kowa ya dawo faloun ba sai bayan sallar isha'i, jugum Kowa yayi tundaga kan Yan uwan marigayiyar har zuwa kan Yan uwan colonel ɗin, zaune ake babu me cewa kowa kala, kamar zaman jiran tsammani. Sai wajen ƙarfe goma da rabi kowa ya tashi don zuwa yasa haƙarƙarin shi ƙasa, colonel ne Yacewa Aayann "Son kaida daughter na kuje ɗakin daka saba sauka, nasa an gyara muku tun tuni" Da sauri Mummy tace "A'a yabarta tazo mu kwana tare kawai" "Mummy Nidai a gurin yaya Aayaann zan kwana" cewar Nawaz tana turo baki waje. Murmushi colonel yayi "to ku tafi Allah ya tashemu lafiya" Itakam mummy shiru tayi tare da yiwa Allah tasbihi a cikin zuciyarta, Lallai nan gaba zata dena zama kusa dasu Aayaan Domin taga kunya zasu riƙa bata. Koda suka isa dakin da mamaki Nawaz ta kalli Aayaan tace "yaya ya naga photunan ka da yawa a ɗakin?" "Ɗakina ne ai dama, kusan shekara biyar kenan da Colonel ya bani shi, duk sanda nazo Abuja ai anan nake sauka" "Nikam wai wace iriyar shaƙuwa ce tsakanin ku?" "Kinsan haduwar jini, haka nan Allah ya dora mishi ƙaunata tun tuni" Aayaan yace tare da janyota ta faɗa a saman ƙirjin shi. Juyar da ita yayi ta koma ƙasa shi kuma yana samanta, hannunshi yasa ya lakuci hancinta tare da cewa "duk tambayar ta mecece?" Murmushi Nawaz tayi Sannan tace "so nakeyi nasan komai game da kai, saboda ina kaunarka da yawa" Peck yayi mata a goshi sannan yace "humm ai baki kaini sonki ba, da ana buɗe zuciya aga yawan adadin ƙaunar da take yi wa wani to Ni nasan zuciyar ki bazata iya ɗaukar tawa kaunar da nake yi Miki ba, soyayyar da nake yi miki ta fara ne tun daga ranar dana fara ganinki a duniya Allah ya dasa ta a zuciyata. Hakanan naji kin burgeni, sosai Naji inason Nasan komai game dake, shi yasa ma naki yarda na maidake gida. Murmushi tayi tare da cewa "Nima haka" "Hmmm ba gaske bane! Saboda kin daɗe kinajin tsoro na, kuma ko son ganina bakyayi" "Kai yaya! Nifa idan na ganka ne sai inji zuciyata na wani irin mugun bugawa, gaba ɗaya saina rasa nutsuwata, wani zubin har ji nakeyi kamar numfashina zai ɗauke musamman idan ka matso kusa dani sosai". Dariya Aayaan yayi "ooh Ashe dai duka abu ɗaya ke ɗawainiya damu, wallahi nima inajin haka, saidai dayake Ni namiji ne shiyasa baza'a gane nawa ba" Hannu yasa ya fara zuge zip ɗin dake gaban rigarta, ai kuwa da sauri Nawaz ta riƙe hannunshi gam tare da cewa "yaya Don Allah kayi haƙuri kabar min riga ta." Be kula taba illah hannunta daya cire ya karasa zuge zip ɗin, tashi yayi ya ɗauketa chak tare da shiga bayin dake cikin ɗakin wanda saika kula da kyau tukuna zaka lura da ƙofar shi. Be cire musu kayanba ya kunna musu warm shower, saida suka jiƙe sharkaf Sannan ya cire nashi kayan, da sauri Nawaz ta rufe Idonta saboda kunya, amma shi sam ko a jikinshi, nata kayan ya cire mata sannan ya fara mata wankan, nashi yayi shima a gurguje Saboda kada ta gaji da tsayuwa, towel guda biyu ya cira a cikin towel rack ɗin dake maƙale a kusurwar bayin, saida ya ɗaura mata sannan ya ɗaura nashi. Chak ya ɗauketa suka fita daga bayin, ita dai Nawaz duk wannan abun da yakeyi idonta na rufe sannan ba um ba um'um, tana jinshi ya shafa mata lotion me uban kamshi sannan ya maida mata da towel ɗin. Saukar turare taji a wuyanta yana fesa mata body spray.. Shima tsaff ya gama gyara jikinshi "dear wannan shiru haka? Ko nayi laifi ne" Kasancewar ta daɗe batayi magana ba hakan yasa muryarta chanza salo "A'a ai baka laifi a gurina, kuma in'sha Allah bazaka taɓa yi ba" "Wow wow wow Nagode sosai Nooroul hayat, gaskiya naji daɗi sosai" Kwantawa yayi tare da nuna ƙirjinshi sannan yace "ƙirji na na maraba dake ako wane irin lokaci" Murmushi Nawaz tayi "Nifa nayi dacen mijin Aure" sannan ta kwanta a saman ƙirjinshi tare na sakin jikinta sosai, tunani takeyi dafa ya mutu da shikenan yanzu takaba takeyi. Da sauri tace "ya Allah na roƙeka ka taimakeni kada abin daya faru baya ya kuma faruwa, idan kuma zai farun to ya Allah ka kasheni kafin lokacin" Toshe mata baki Aayaan yayi domin yasan meta tuna take wannan sumbatun. "Dear idan kika mutu ai nima na mutu, in'sha Allah ba yanzu ba, sai mun aurar da little Aayaan da ƙannenshi" Shiru tayi tanata wasa da kwantaccen gashin daya cika mishi hannunshi har zuwa yatsu, baƙiƙƙirin dashi sai ƙyalli yakeyi a saman golden skin ɗinshi, ga fatar hannun tuɓus don taushi, sosai hannun ya burgeta taketa wasa da gashin. Maida kanta tayi ɗaya gefen ta Fara wasa da gashin ƙirjin shi wanda ya kwanta tundaga saman ƙirjinshi har zuwa marar shi, a hankali Aayaan yaji mood Dinshi na chanzawa, bata dena ba illa cewa da tayi "yaya meyasa mata basada irin wannan gashin" Murmushin ƙarfin hali yayi domin ta fara sukurkutashi, daboda ji yakeyi kamar tana yi mishi tafiyar tsutsa "kai dear, akwaiki da Abin dariya, yanzu idan wannan gashin ya fitowa mata ai bazai yi musu kyau ba sam" "Amma ai kai yayi maka kyau sosai" "Really" Murmushi Nawaz tayi "yea Really" Tun yana daurewa har saida yace "dear pls kidena wasa da gashin nan, I feel uncomfortable" Bata yarda ba illa ma saita ɗauki Abin a matsayin wasa "kai yaya nikuma birgeni yakeyi Sosai Allah" ci gaba tayi da wasanta ko a jikinta. Ganin tanaso sai ya kyaleta kawai be kuma mata magana ba, daga ƙarshe dai dayaga bazai iya jurewa ba sai kawai ya birkita ta zuwa ƙasan shi, wasanni ya fara yi mata masu zafi kuma waɗanda suke ɗauke da zallar ƙauna da mararin juna. Anan ne Nawaz ido ya fara raina fata, "Nifa yaya gaskiya kaga ka Bari, nidai banason irin wannan wasan naka me dogon zango, sai ayi awa uku ana abu ɗaya!" Ganin zata fara ihu sai kawai ya haɗe bakinsu guri ɗaya. Tun tana iya neman kwatar kanta da sassan jikinta har saida jikin ya koma yayi laushi yadda ko hannu bata iya ɗagawa. Yau kam Nawaz taga ta kanta, kuma ta ƙara raina kanta, domin irin wasan da yake yi mata ya zarce na kowane Lokaci domin numfashinta har ɗaukewa yakeyi, hawaye ta fara yi ko zataji sauki a ranta amma ina babu wata mafita domin Aayaan ya gama haukace mata baki ɗaya. Wannan karon koda yazo yin introducing ɗin kanshi Saida yaji tamkar first night ɗinsu, sosai Aayaann ya kuma angoncewa Inda ita kuma Nawaz ta sharɓi kuka har ta gaji. Ya rasa meyasa yake samun wata irin gamsuwa da nishaɗi a duk sanda zai Mu'amulanci Nawaz, jinshi yakeyi kamar sabon mutum, bayada wata matsala ko kaɗan, kuma sai yake jinshi cikin nishaɗi. Ansha fama inda da kyar Nawaz ta yarda yayi mata wanka ya gyara mata jiki, fushi kawai takeyi da kumbure-kumbure Shammatarshi tayi zata fita daga ɗakin da gudu, Allah yasa yanada hanzari ya chafketa, matseta yayi a ƙirjinshi har saida tayi barci. "Ohh dear Sarkin rikici da rigima, ita kuma har dai anason aga fushinta to a mu'amulanceta, while wasu matan kuma su burinsu ma ayita mua'mulantar tasu, hakan yana nufin ita ba jarababbiya bace kenan? And kuma wasu matan har kai mazansu ƙara sukeyi akan basa musu wasa kafin jima'i amma ita kuma wasan ne bata so" Hakanan ya gama zancen zucinshi inda shima barci ya kwasheshi. Da safe da aka tashi anata fama za'a hura wuta saboda anaso a ɗora Abincin da za'ayi sadaka amma wuta taƙi huruwa, da'an hura sai ta mutu, dai-dai lokacin Nawaz ta fito sanye da abaya baƙa ta yafa mayafinta, saida ta gaisa da kowa tukuna ta ƙarasa inda ake cuku-cukun hura wutar. Sosai ta zage ta gyara itatuwan ta haɗa kansu, sai gashi cikin ƙanƙanin lokaci wutar ta huru, kama babbar tukunyar sukayi ita da wata suka ɗora sannan suka fara ɗebo ruwa suna zubawa. Aayaann wanda ke tsaye a bakin window tun fitowar Nawaz ne yaga Abin yayi yawa, fitowa yayi yaje gurin Mummy yana sosa ƙeya. "Ya akayi ne" mummy tace donta lura akwai Magana a bakinshi. "Mummy dama naga tunda dear ta fito sai aiki take yi kuma gashi batada lafiya and jiya bata samu barci isassheba" Shiru mummy tayi tana jinjina wannan lamari, "wai me yaran zamani suka zama ne? Anya sunsan me suke aikatawa ma kuwa? Itafa kunya neman kasheta takeyi Amma su ko a jikinsu, kuma dama tun fitowar Nawaz ɗin ta lura da idonta ya chanza kala Sannan kuma taga tafiyarta ba dai-dai ba, Alamun dai Aayaan ɗin ya matsa mata, sai gashi kuma yazo ya tabbatar mata da hakan da kanshi. "To kaje zan hanata yanzu idan naje gurin" Rungumeta yayi tare da cewa "thank you very much mummy" Tsaye tayi tana kallonshi baki sake har ya koma ɗakin, wato anyi rasuwa suda sukazo gaisuwa amma shi shagalinshi yakeyi, mutumin da daba don shan ruwan shi be ƙare ba da yanzu yana kabari, jinjina kai kawai tayi ta fita zuwa inda Nawaz ke aikin don dakatar da Ita. Koda tayiwa Nawaz ɗin magana cewa tayi taji sauki zatayi "mummy Naji sauƙi kuma Kinga idan bamuyi ba nasan kece zakiyi, to don Allah meye amfanin gamu kuma kizo kina wahala. Sosai mummy taji daɗin yadda Nawaz ta nuna tasan girmanta da darajar ta, dai dai nan Aseey ta fito riƙe da hannun muhsien yana rikici. Aikuwa yana hango Nawaz ya nufeta da gudu yana dariya "Aunty zo muje kitchen ki haɗa min smoothie " "Yauwa kuje daughter, saiki haɗa harda mijinki shima yace zaisha" Cewar mumy don neman hanyar da Nawaz ɗin zata bar wajen. Haka aka wuni Nawaz taƙi bari su haɗu da Aayaan, ko ritsa ta yayi a guri kwasa takeyi aguje ta gudu, sai dai ya tsaya yana dariya da mamaki. Haka da dare ma sanda za'a je a kwanta Nawaz tabi su mummy, waigowa mum tayi tare da cewa "daughter kibi mijinki kuje ku kwanta mana" "Ni dai mummy bazan bishi ba, dake zan kwana" "Haba dear kizo muje mana, jan ajin ya isa haka" cewar Aayaan don Neman hanyar da zai basar da zancen. "Nidai bazan bika ba tunda idan nace kadena banaso baka denawa" Ba shiri Mummy ta ƙara sauri Don kada kunnenta ya jiyo Abinda yafi ƙarfinta, ita kuwa Aseey dariya taketa kunshe wa tare da cewa "Anzo wajen, ai jiya Saida akace ki bimu amma kika ƙi waike me miji, to ai gaki ga mijin nan, duk a zuciya take wannan zancen. Tana shiga ɗaki ta rufe ƙofa saboda kada Nawaz ɗin ta shigo. Aikam ihu Nawaz ta fara tana cewa "Mummy Don Allah ki cewa Aunty ta buɗe kofar nan wallahi daukata zaiyi kuma Ni banso..... Kafin ta ƙarasa tuni yayi sama da ita yai Hanyar dakin su, sai wuntsil wuntsil takeyi tana cewa "ka sakeni, ka ajiye Ni, babu ruwana dakai " °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *ZARIA........* Koda ummin Nawaz ta koma gida, tsaff ta samu umma, sosai taji daɗi ganin ciwon nata sai sauki yake Daɗa yi, amma Abinda yake ɗaga mata hankali shine har yau umman bata iya tafiya koda kuwa an kamata an miƙar da ita ne. Ɗan Abinda ba'a rasa ba ta gyara, na kawar wa ta kawar, Sannan tacewa fauziyyah ta tafi gida ta ɗora wa yara abinci inda itama ta ɗora tata sanwar. Ta gama haɗa duka haɗin shinkafa da wake dafa Duka, ɗebo shinkafar tayi taje gaban pampoo ta kunna ruwa don wankewa, sakin robar shinkafar tayi ta tsaya tana Binshi da Kallo. Kusan wa ta gani??? Abban Nawaz taga ya shigo gidan hankali tashe kamar wanda zai tashi sama. Shima tsayawa yayi ya zuba mata ido, mamaki yake yi Wato Rahma akwai rikon alƙawari, duk tsawon lokacin nan da baya nan bata koma gida ba kenan? Kuma yafi kowa Sanin cewa ba dadin gidan takeji ba sanda ma yakenan balle sanda bayanan.. Hawayene ya fara bin kuncinsu, kowa da Abinda yake kitsawa a cikin zuciyarshi. *NAGODE, NAGODE, NAGODE SOSAI DA NUNA KAUNA DA KULAWA, HAƘIƘA NAJI DAƊI SOSAI KUMA NA YARDA ALLAH SHIKE BAKA MASOYA, DOMIN NAGA KIRA BILA ADAD HAKA TEXT MESSAGE SUMA BA ADADI, INA GODIYA DA NUNA KULAWA, ALLAH YA BAR ƘAUNA DA ZUMUNCI* *MATAR RASHEED*✍️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *85* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* _Assalamu alaikum_ _Ina yiwa kowa Fatan Alkhairi, da fatan munyi Sallah lafiya, Allah ya amshi ibadun mu (AMEEN)_ _Bayan hutu da mukayi na Ramadan, Allah cikin isar sa da mulkinsa ya ƙara bamu aron rai yau cikin ikon shi zan cigaba da littafina mai suna *SARFRAZ* Allah ya bamu ikon gama shi lafiya *(AMEEN)*_ _duk da dai dama saura pages ƙalilan mu kammala, Wanda daga bisani zan cigaba da posting ɗin ɗayan littafina mai suna *IZAYAR RAYUWA* In sha Allah_ Da gudu Ummin Nawaz ta tafi ta faɗa cikin ƙirjin shi, Sosai kuka ya kuma kwace mata "dama kana raye? Dama Zan kuma ganin ka? Dama da rabon ganawar mu?" Riƙe ta Abban Nawaz yayi sosai a cikin jikinshi, tun daga cikin zuciyarshi yakeji kamar wani Abu na fita tare da duk wata damuwa daya daɗe a ciki suka kwararewa a ƙasa, sakayau haka ya koma jinshi "Rahma nayi kewarki, nayi kuka da idona duk a kanki, ko Yanzu tararrabin shigowa gidan nan na gama yi a waje Kafin na shigo, domin duk iya tunanina na aje cewa bakya Cikin gidan nan" Duk wannan abin dai Ummin Nawaz na cikin jikinshi taƙi sakin shi Riƙe ta yayi Sosai sannan ya fara tafiya yana nufar hanyar dakin su "muje in samu in ɗan zauna kona samu na dawo dai-dai masoyiyata!" Kunya maganar taba Ummin Nawaz "wai masoyiyata" _Ni kuwa matar Rasheed nace "Ai soyayya bata tsufa, Gara dai shima ya ɗan taɓa"_ A saman three sitters sofa ɗin dake faloun ya zauna, ajiyar zuciya yaketa saukewa a jejjere kamar yaron dayasha kuka ya godewa Allah. Kafin wasu mintuna tuni ummin Nawaz ta cika mishi gaba da abubuwan motsa baki, "Allah Sarki Rahma mai karamci! Ashe dai har yanzu baki chanza ba?" Cewar Abban Nawaz yana ɗaukar Ruwan data ajiye mai yana buɗewa. Jikinta har rawa yakeyi tsabar farinciki, Kamar a mafarki haka take ganin komai, wai yau itace gata ga Muhammad dinta har yana yaba mata akan ta kawo mishi wani abuu, ciki ta shiga ta kuma auno wata shinkafar ta wanke ta zuba Sannan ta leka ɗakin umma don ta gaya mata Abban Nawaz ya dawo, ganinta tayi tana barci kuma da alamun barcin yayi mata daɗi, kyaleta tayi bata tasheta ba, ta juya ta koma ɗaki, koda zata shiga da sassarfa ta shiga ɗakin saboda yadda takejin idon Abban Nawaz akanta. Hakanan ta samu kanta da wata irin jin kunya da nauyin shi gaba ɗaya sun lullubeta, "ina yini?" Ummin Nawaz tace a ɗan ɗarare, domin bata saki jiki a saman kujerar data zauna ba. "Lafiya Lau hasken idaniya ta, fatan na sameki lafiya?" Dan murmushi tayi tana ganin kamar ya ɗan chanza saboda yadda yaketa faman zolayar ta tunda suka haɗu, daga bisani kuma tace "lafiya Lau Alhamdulillah, ya bayan saduwa?" "Hmmm Rahma babu daɗi, Bama naso na tuna samm.." "To Allah ya kyauta ya kiyaye gaba" "Ameen Rahmatullah" cewar Abban Nawaz yaya zancen zuci cikin zuciyarshi "Lallai Rahma har yanzu baza ta chanza ba kenan daga wannan kawaicin nata da yakana" yasan muddin bashi ya faɗa mata abubuwan da suka faruba, da Dalilin rashin dawowarshi ba to tabbas ita bazata taɓa tambayar shi ba.... Domin ita a nata gurin zata ga idan ta tambaye shi zaiga kamar tana ƙalubalantar shine. Nan ya matsa kusa da ita ya zauna ya fara bata Labarin abubuwan da suka faru bayan tafiyar shi har zuwa yanzun ɗaya dawo gida, shiru kawai tayi tana girgiza Kai tare da ƙara amanna da buwayar Ubangiji "lallai duk abinda Allah ya tsara babu makawa saiya faru, koda kuwa duka duniya zasuyi tawaye akan abin. Bata Ankara ba saijin ƙauri tayi, shinkafar da take dafawa har ta fara konewa domin ita sam tama manta da ita. Fita tayi da sauri ta sauke Sannan ta kwashe wadda bata ƙone ba ta zubawa Abban Nawaz a plate sannan ta zubawa Umma itama, ɗakin takai mata ta ajiye saboda har zuwa lokacin bata farka ba. In takaice muku zance dai, Abban Nawaz dai be nemi umma ba kuma beyi maganar taba, koda Ummin Nawaz tayi mishi magana cewa yayi "Rahma Don Allah kada ki bata Min rai, ina cikin farin ciki fa, kuma angoncewa nakeso muyi bayan na watsa Ruwa, kuma wallahi yau sonake a kaini inda ban taɓa zuwaba domin shekara daya ba kwana ɗaya bace, nayi kewarki sosai, "ina ummina?" Murmushi ummin Nawaz tayi Sannan tace "umminka tana gidan mijinta.." A maimakon ya nuna bacin rai sai ya nuna farincikin shi a fili, har sujada yayiwa Ubangiji "lallai addu'a bata taɓa faduwa ƙasa banza, Allah Nagode, Nagode, Nagode maka sosai." Abinda Abban Nawaz keta maimaitawa kenan Mamaki ne kecin Ummin Nawaz, sak Muhammad ɗin data sani baya Kafin ta haifi Nawaz shi take gani yanzu, dadine har cikin zuciyarta, maganar da yayi ta cewa nayaso ya Angonce ita ta ƙara bata kunya sai tayi sauri ta miƙe Domin shiga ɗaki, abin kuma da yayi najin cewa anyiwa Nawaz Aure sai yasa ta tsaya tana Binshi da Kallo cike da jin daɗi da mamaki. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Aayaan be direta a ko ina ba sai saman gado, "Nifa yaya ka rabu dani, nace maka ba anan zan kwana ba amma saida kasan yadda kayi ka kawoni, Alhalin idan nace maka banaso ba bari kakeyi ba" "Wallahi Sweetheart nasan bazan iya barci bane idan bakya kusa dani shiyasa kika ga na matsa, amma idan zan takura miki to ki taso na maidake" shiru Nawaz tayi tana ganin idan tace zata koma ɗin lallai bata yi mai adalci ba "na fasa zan kwana anan ɗin kawai, amma promise bazaka yi min komai ba?" "Dear kenan! Babu abin da zanyi Miki, kuma ko jiyan ma aike kika ja har hakan ta faru, Ni Sam banyi niyar yi miki wani abuba har zuwa mu koma gida, amma saida kika susutani ya zamana nemarwa kaina mafita kawai nakeyi lokacin" cewar Aayaan yana zama a gefen ta tare da miƙe ƙafafunshi a saman gado. Bata tanka shiba duk da taji duka abinda yace, Duba takai zuwa yatsunshi, tunda take bata taɓa zaton sun kai haka tsawo ba, ga wasu irin kwantattun gashi bakake sidik a saman yatsunshi da kuma gefen ƙafar shi "yaya wai dama haka yatsun kafarka suke da tsawo kamar na hannu? Kai Allah waɗan nan ma sai su iya fin na hannun wani tsawo." Hannu takai zata riko yatsun, ai da sauri Aayaan ya janye ƙafar domin yasan idan ya barta zata kuma jagwalgwala shi ne kuma ya nemi sauƙi ita kuma tace ya matsa mata. "Yaya ka bari in gani pls" "Nope muje muyi wanka tukuna" be saurari me zata ce ba ya sunkuceta yayi cikin bathroom ɗin da ita, ko a bayin ma a gurguje yayi musu wankan saboda shi kadai yasan abinda yakeji akanta. Koda suka fito basu shafa koda mai ba, haka zalika towel ne kadai a jikinsu ya ja musu bargo suka rufa, inda Nawaz take rumgume a ƙirjinshi yana bubbuga mata baya ahankali don ya samu barci ya ɗauketa da wuri. Cikin ikon Allah kuwa ba'a ɗauki lokaci mai tsawo ba barci ya ɗauke ta, shima ganin tayi Barci saiya daɗa gyara mata kwanciya Cikin ƙirjinshi tare da rungumeta Sosai, a haka shima barcin yayi gaba dashi. Dai-dai Kiran sallar asbah Aayaan ya tashi, cike da ƙauna da soyayyah ya tashi Nawaz don suyi raka'a tainil firij kafin ya tafi masallaci. Koda ya dawo daga masallaci bega Nawaz a cikin ɗakin ba, mamakine ya kamashi "to ina zata da asbar farii" *CIGIYA* *CIGIYA* *CIGIYA* *Don Allah akwai wata wadda mukayi magana zan sai frame's a gurinta kafin sallah, to matsalar da aka samu itace banyi saving ɗin Number dinta ba kuma sai Whatsapp ɗina ya samu Matsala, yanzu haka na rasa contact dinta, to dayake dama tana bibiyar wannan littafin, to Don Allah idan taga wannan cigiyar tayi min magana ta wannan Number 08093215055,* Nagode Matar Rasheed ❤️*🎀🎀SARFRAZ🎀🎀* *86* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Fita yayi daga ɗakin ya dudduba waje ko zai ganta a wani guri, duk inda ya duba be ganta ba sai kawai ya koma ɗaki domin yasan bazata wuce ɗakin su Mummy ba. Ita kuwa Hajiya Nawaz tana chan bayan gida inda aka hura wuta jiya, wuta ta hura Sannan ta ɗora babbar tukunya inda ta ɗauki bokiti ta riƙa debo ruwa a fampo tana zubawa har saida ta kintaci dai dai wanda tasan zai isa dama kunun Sannan ta barshi haka, murfi tasa ta rufe tukunyar, inda taga mummy ta debo waken da akayi kosai jiya ta shiga ta auno tiya Uku, a hankali a hankali ta riƙa zubawa a turmin tana surfawa har saida ta gama Sannan ta kaishi bakin fampo ta ajiye, cikin store ɗin ta koma ta buɗe babban bawon da gasara ke ciki ta kwashe ruwan saman sannan ta ɗibi bokiti ɗaya da rabi ta rabashi gida Uku ta ajiyesu a bakin tukunyar inda Ruwan keta tafasa, cikin store ɗin ta koma ta dauko wani madaidaicin bokiti wanda zata rika dibar Ruwan zafin tana zubawa a cikin gasarar. Cikin mintunan da basufi Goma ba ta gama dama kunun tsaff, murfi tasa ta rufe bokitan Sannan ta kuma ɗebo ruwa ta zuba rabin tukunyar ta rufe. Bakin fampo ta koma domin ta wanke wake, a daidai nan mummy ta fito domin ta hura wuta ganin garin ya fara haske. Mamaki ne ya kamata ganin manyan bokitai har uku cike da kunu, ga kuma wani ruwan a cikin tukunya shima yana shirin tafasa. Ƙarar Ruwan dataji a lungun da fampo yake yasa ta ƙarasa da sauri, Nawaz ta gani a duƙe tana wanke atarugu da tattasai tana zubawa a cikin waken data gama wankewa... "Lahaula wala quwwata illah billah! fisbilillah daughter dama kece kiketa faman wannan aikin? Kin manta kedin ba wata cikakkiyar lafiya ce dake ba! Maza bar aikin nan ki koma ɗaki ki kwanta ki huta Nagode sosai sosai, Allah ya saka da Alkhairi kinyi kokari sosai.." "Allah mummy naji sauƙi, kuma Ni kwanciyar ce bana so, don Allah ki barni saiki cigaba Ni kuma ina tayaki " Bayanda mummy ta iya ganin Nawaz ɗin ta nace saitayi, sai kawai ta kyaleta bata kuma yunkurin hana taba "daughter bari to naje na kira su Fudail suzo sukai nikan waken" "To mummy saikin dawo" cewar Nawaz tana ɗaukar bawo a bakin fampo tare da yin haryar store, shinkafa ta auno tiya biyar ta wanke ta zuba kafin Mummy ta dawo. Koda Mummy ta dawo faɗa tahauta dashi, "haba daughter! Yaza'ayi ki riƙa daukar abuu mai nauyi haka bayan kinsan cikin condition ɗin da kike!" Riri rimi Nawaz tayi da ido tare da cewa "Mummy shinkafar kawai fa zan dafa ke kuma sai kiyi miyar" Jinjina kai kawai mummy tayi tana mamakin ƙarfin halin Nawaz. Cikin awa daya har tayi perboil ɗin shinkafar ta maida ita ta tirara, lokacin ma har Nawaz tayi nisa da suyar kosai da tayi kane kane ta hana mummy yi, ganin haka sai Mummyn ta hura mata wata wutar saboda idan akace sai an jira shinkafar ta dahu kafin a fara suyar to za'a bata lokaci sosai gashi gari ya fara wayewa. Itama mummy gasara tasawa kunun Sannan ta zuba sugar yadda kowa sai dai kawai ya dibi yadda zai mai, itama Nawaz a cikin warmer take zuba kosan data soya. Duk mutane sun fara cika gurin saboda sai fitowa suke suna diba domin su karya, Itama Nawaz ta gama soya kaskon ƙarshe tana tunanin yadda zata sauke man da tayi suyar dash Naufal ya fito yana dariya "Aunty yau ashe better kikace muci! Wannan irin Natural delicacies haka" hakanan Allah ya ɗora musu son Nawaz da ganin girmanta tun lokacin da sukaje Zaria. Murmushi mai kamar dariya Nawaz tayi tare da cewa "Nidai bar wannan tsokanar taka ka taimaka ka daukemin man nan ka kaishi store ka adana Saboda da zafi Sosai kada wani ya ƙone" Sara mata yayi Irin na wasa Tare Da cewa "an gama ranki ya dade matar Captain" Girgiza kai kawai tayi tana mamakin yadda suke mu'amulantar ta kamar dama sun santa tun tuni.. Towel yasa ya ɗauke kaskon a saman wutar yayi hanyar store ɗin tare da cewa mutane "a kauce mai ne me zafi" Ƙoƙarin tashi Nawaz tayi saboda tanaso ta samu ta watsa ruwa saita ɗan kwanta kafin akira Sallar azahar, mikewarta keda wuya wani irin jiri ya rufe ta cikin ƴan dakiƙu duhu ya baibaye idonta baya tayi zata faɗi Allah ya taimaka daidai lokacin Naufal ya dawo daga kai man, shi yayi sauri ya tareta cikin hanzari. Cikin sauri da karsashin da mummy batasan tana dashi ba ta karaso gurin cikin tashin hankali "Naufal meya sameta?" "Mummy wallahi nima kawai gani nayi zata faɗi shine na rike ta" cewar Naufal Muryar shi na nuna alhini akan abinda ya faru, kuma still dai yana rungume da Nawaz a jikinshi.. Kafin wani lokaci Mutane duk sun iso gurin suna ta yi mata Allah ya kyauta da sannu, amsarta mummy tayi ta jinginata da jikinta sannan ta nufi ɗaki da ita donta samu ta kwanta, tasan aikin data cikawa kanta ne yasa hakan ya faru. Mamakin Son barci da son jiki irin na Aseey Mummy take tafe tana yi "wato har Yanzu barci takeyi shiyasa bata fito ba kenan, ita dai Aseey sai kace bata girma ba, fisbilillah Nawaz kwara nawa take da har tasan ta tashi ta ɗora Abinda mutane zasu karya dashi?" A cikin corridor Mummy tayi kaciɓis da Aayaan, tsaye yayi yana karewa Nawaz ɗin kallo tare da mamakin Me ya faru mummy ke rungume da ita sannan daga bisani, yace "mummy me ya faru naga dear wani iri?" "Mikewa tayi bayan ta gama soya kosai kawai sai gani mukayi tayi baya zata faɗi, to Allah ya taimaka Naufal na kusa ya rike ta" Tsoro ne ƙarara ya bayyana a fuskar Aayann "Mummy faduwa fa! Innalillahi wa'inna alaihi raji'un, yanzu meyasa hakan ta faru?" "Wallahi nima dai ban sani ba, amma dai ya kamata kuje asibiti a duba ta. "To mummy In'sha Allah" Ɗakin Aayaan mummy ta kaita saboda zatafi sakewa tunda babu kowa a cikin ɗakin balle a dameta da hayaniya. Mummy na fita Aayaan ya ƙarasa ya dago Nawaz ɗin zuwa jikinshi "dear idan nace ki bar Abu please ki taimakeni ki riƙa bari, yanzu da wani Abu ya sameki fa? Kuma kinsan ba cikakkiyar lafiya ce dake ba" Ciki murya dishi dishi Nawaz tace "I'm sorry sweetheart, wallahi bawai banajin Maganar ka bane, kawai dai banaso Mummy ta wahala ne saboda idan banyi ba Nasan dole ita ce zatayi." "Hmmm shikenan!! Thanks for the love and care... Amma dai ya kamata ki dena pls" Bata kuma cewa komai ba har zuwa sanda ga sunkuceta yayi bayi da ita don yayi mata wanka. Cikin ƙasa da mintuna Talatin ya shirya su, ɗaukar Nawaz ɗin yayi ya ratso ta tsakar gidan be damu da Yadda mutane ke Binshi da ido ba, shi yanzu ta lafiyar matarshi yakeyi bata Kowa ba. Bayan sun yi sallama da Mummy ne ya buɗe ɗaya daga cikin motocin dake Parke a parking space ya saka Nawaz a seat ɗin me zaman banza Bayan ya ɗan kwantar mata da seat ɗin, shiga driver side yayi ya figi motar zuwa wani babban private hospital wanda yake mallakin abokinshi ne wanda sukayi karatu tare. Yan mintoci ne ya ƙarasa dasu dayake babu nisa daga gidan colonel ɗin. Direct office ɗin Dr Uthman ya karasa, bayan ƴan gaishe gaishe da ya Bayan rabuwa Aayaan ke sanar da shi Abinda Ya samu Nawaz, sannan ya ƙara da cewa "friend mata nakeso su duba ta ba maza ba, "bakada matsala abokina" cewar doctor uthman yana ɗaukar wayarshi dake ajiye a saman desk Nurses biyu Dr uthman ya kira suka tafi da Nawaz bayan ya faɗa musu Abinda zasuyi haɗe da basu wata takarda da ya danyi rubuce rubuce a jiki. Aayaan na zaune a office ɗin Dr uthman ne amma zuciyarshi is out there, damuwa da fargaba ne ke Nuƙurƙusar shi, tsoro yakeyi kada ace wani abu gagarumi ne ke damun Nawaz. Duk hirar da uthman keyi mishi babu Abinda yake ganewa aciki, illah dai yasan bakinshi na bada amsa. Saida ya sauke wata iriyar nannauyar ajiyar zuciya sanda yaji sallamar daya daga cikin nurses ɗin da suka fita da Nawaz, ɗan rusinawa tayi bayan ta shigo sannan tace "sir Doctor dejert ce tace nazo na faɗa maka wai tanaga sai anyi mata ultra sound" "No problem! Ayi duk Abinda Ya dace, nidai burina a gane meke damunta" Aayaan yaba nurse ɗin amsa Kafin Dr uthman ya bata. Murmushi Dr Uthman yayi sannan yace "kinji Abinda mijinta yace, so ya gama magana, U can go." Bayan kamar minti 35 Nawaz ta shigo office ɗin tare da taimakon wata nurse guda ɗaya, da sauri Aayaan ya mike yana gyara kujerar da Nawaz zata zauna akai. Murmushi nurse ɗin tayi tare da risina tana mikawa Dr Uthman wata takarda sannan ta juya ta fita. Bayan ya gama karantawa ne ya mika wa Aayaan takardar Fuskarshi ɗauke da matsanancin murmushi... Aayaan be jira ya gama karanta takardarba ya fadi ƙasa yayi wa Allah subhanahu wata'ala sujuda ba Tare daya damu da Kasancewar a inda yake ba. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ummin Nawaz itama tunda gari ya waye Abban Nawaz keta tattalin ta, komai ya hanata yi, data yunkura zatayi abuu sai ya hanata, ko kuma shi yayi sauri yayi. Duk sanda suka haɗa ido kuma saiya sakar mata wani irin sassanyar murmushi, mamakin yadda komai nata baya tsufa yakeyi, domin kuwa kamar yadda yace Amarci zaisha to kuwa haka yasha Amarcin Domin kuwa Ummin Nawaz bata yi sanya ba a daren bayan ta haɗa mishi ruwan wanka ya shiga bayi itama ta samu ta ɗan yi gamje gamjen mu na mata ta haɗa kanta Emergency, tunda dama bata yarda ta zauna batare da kayan gyaran jiki a ɗakin taba, balle wannan karon bata daɗe da dawowa daga Maiduguri ba. Bayan sunyi wanka sun shirya ne Abban Nawaz yacewa Ummin Nawaz tazo suje ɗakin Umma akwai maganar da yake so suyi. Da sallama ya ɗaga labulen ɗakin umma ya shiga ciki Ummin Nawaz na biye dashi, umma ko sakin baki da hanci tayi tana kallonshi kamar a Cikin mafarki, bata daɗa tabbatarwa cewa ba mafarki take ba saida taji yace "Butulu! Hakan da nazo na sameki ya daɗa tabbatar Min da gaskiyar Komai," Girgiza kanshi yayi sannan yaci gaba da cewa "Hmmm! Ban taɓa tunanin cewa da makiyiyata nake zaune ba saida Allah ya fallasa min komai, ya fito da Komai a fili kuma ina ƙar......... Kuyi hakuri da jina da kuka yi shiru, munyi sha'ani ne Kusan kashi uku a jere, yanzu haka ma bamu gama ba, Don haka nake ƙara baku haƙuri ba lallai ku riƙa jina kullum ba sai in Allah yasa na samu lokaci Matar Rasheed ❤️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *87* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Kuma ina ƙara yiwa Allah godiya daya lalata Abin ba tare da nima na cutar da wani ba, kin cuceni! kin cuci Rahma, kuma duka akan Abinda Allah be haramtaba, daga baya kuma kika maida kiyayyar taki kan me sunan mamana. Tunda Madina ta buɗe ido a cikin duniya take cikin kuncin rayuwa, Abin be tsaya nan ba har saida kikasa ƴan uwanta na jini suma suka tsaneta, yanzu to wa gari ya waya..? Waye ya koma Abin tausayi kuma abin ƙi ga kowa? Ke kanki kinsan idan ƴan Uwanki sukasan da wannan maganar to kin zama Abin gudu, babu wanda zai yarda ki raɓe shi. Waigowa yayi ya kalli ummin Nawaz sannan yace "wai ko Rahma kinsan cewa ita tasa akamin asirin da zai tafi da hankali na yasa na manta komai da kowa? Sannan bata tsaya iya nanba saida tasa aka min shashatau akan ku ta yadda zan watsar da lamarin ku baki daya! Kuma fa wai duk hakan akan kishi tayi shi?" "Kayi hakuri ranka ya daɗe! (Dama tun tuni haka take ce mishi), nidai na yafe mata kuma zansa Nawaz ta yafe mata, sannan kaima ina rokonka Alfarma akan ka yaf........" "Dakata Rahma! Wai ke kuwa wace irin zuciya gareki wadda bata fushi? Ni dai bazan iya yafewa ba, idan ma na yafe to taje na saketa domin bazan iya ci gaba da zama da ita ba" "Innalillahi wa'inna alaihi raji'un, haba Abban Nawaz meyasa zaka yanke hukunci cikin fushi, ya kamata ace ka samu lokaci kayi tunani tukun kafin kace komai game da wannan maganar" "Wane tunani kuma zanyi banda wanda nayi a baya? Ai iya tunanin da nayi da ƙuncin dana shiga sun isheni, Kuma Ni Sam ba'a cikin fushi nakeba, domin da a cikin fushi nake Wallahi zan iya rufeta da duka har saita dena motsi, Rahma wai ko kinsan me na gani?, Kinsan halin dana shiga? Kisan irin ciwon da zuciyata ta ƙunsa? Haka fa rayuwata ta koma banida maraba da mahaukaci, in banda Allah ya haɗani da malamin kirki mutumin ƙwarai, wanda yasan meye malinta kuma yake amfani da ilimin da Allah ya bashi wurin temakon al'umma da yiwa addini hidima, shine fa ya tsaya tsayin daka sai daya karya duka sihirin data yi min, amma ai da tuni na dade ta fara hauka tuburan" "Abban Nawaz don Allah adena tone tone, muma masu laifi ne a gurin Ubangiji, ya kamata ka yafe mata dalilin hakan sai Allah ya ƙara shiryata kuma kaima ya yafe maka." Umma wadda tunda suka shigo bata furta komai ba illa hawaye da yaketa kwarara daga cikin idonta, bata taɓa jin kunya da nauyi irin na yau ba, lokaci ɗaya tsana da ƙyamar kanta da ayyukan ta suka saukar mata, nadamar da tafi wadda tayi a baya ita ta cika cikin ƙwaƙwalwarta. Sosai ta ƙara fashewa da kuka jin irin kalaman da mijinta keyi akanta, lallai ta tafka babbar asara a rayuwarta, yanzu bazata iya nuna wani abu me kyau da zatace itace ta aikata shiba domin kiyamarta, gaba ɗaya ta shagala da duniya wadda kuma ba matabbata bace. Cikin gunjin kuka tace "Muhammad Nagode maka sosai, Allah ya saka maka da Alkhairinsa, kuma hukuncin daka yimin wallahi na chanchanci fiye da haka, amma Nasan adalcinka ne yasa haka domin Ni shaida ce akan kyawawan dabi'un ka .... Nagode sosai sosai, amma ina ƙara baku haƙuri dukanku musamman Rahma da Nawaz, na cutar dasu iya karfina, sannan mama (tana nufin mahaifiyar Abban Nawaz) sai kai, Don Allah ku taimakeni ku yafe min dukda cewa banida tabbacin cewa Allah zai yafe mini" Da sauri ummin Nawaz ta katseta da cewa "A'a umma kidena cewa haka! Domin wallahu gafurur Raheem," Abban Nawaz ne yayi saurin katse ummin Nawaz da cewa "kuma shadidul iqab ba" Ƙara rushewa da kuka umma tayi tana girgiza kanta cike da nadama da dana sani! Sallamar inna talatu (kawar ummin Nawaz wadda Nawaz ta gudu gurinta) ce ta cika tsakar gidan.. Jikin ummin Nawaz ne ya hau rawa sanin cewa talatun ta dawo da Jamila ne, saboda sanda zata tafi maiduguri gaisuwar Aayaan, (lokacin da aka ce ya mutu) takaita can don bataso masu zuwa gurin umma su ganta da ciki, domin abin har Ita da Nawaz zai yiwa illah. Da sauri ta tashi ta fita daga ɗakin Umma ba tare data nemi izinin kowa ba, da ido tayiwa jamila nuni akan ta shige dakinta, "Rahma ki barsu su karaso Kawai domin abinda na shuka shi nake girba, shine fa mahaifinta to boye boyen me za'a yi?" Abinda Umma tace kenan bayan ummin Nawaz ta fita... "Meye boye boye? Kuma meye Abinda kika shuka?" Abban Nawaz yace tare da ɗaga labule don ganin su waye a tsakar gidan Wani irin sarkakken tari ne ya sarƙe shi sanda ya sauke idonshi akan Jamila "innalillahi wa'inna alaihi raji'un, Yanzu yata ce dauke da cikin shege? Ko aure tayi sanda bananan?" Kowa shiru yayi an kasa samun wanda zai bashi amsa, illa Umma data goge hawayen idonta taci gaba da cewa "Ni Nasan da wuya idan Allah zai yafe mini, barakar dana jawo da gurɓata abubuwan da nayi sunyi yawa" Be tanka ta ba illah janye jiki da yayi ya shige kuryar dakin ummin Nawaz sannan yasa sakata ya rufe kofar. Bakin ciki ne fal zuciyarshi yana taradadin meye ma ya hadashi da umma da har yayi sha'awar aurenta? Ummin Nawaz kuwa jinta takeyi Komai ya dagule mata, Ummah kuka jamila kuka, shikuma ya shige ɗaki ya kulle,. Bata gama wannan zancenba saiga fauziyyah ta shigo da sallamarta a bakinta. Turus tayi ganin yadda Kowa yayi tsuru tsuru, kallon ummin Nawaz tayi tace "Ummi meye ya faru?" Kafin ummi ta furta komai umma tace "Mugun Abin dana aikata shi ya dawo min kuma nake amsar sa koda ban shirya ba, Abban ku ya dawo kuma yace na tafi gidan mu, sannan yaga cikin dake jikin Jamila °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Yana mikewa daga sujudar ya ƙarasa gaban Nawaz, haɗe hannuwanshi cikin nata sannan ya fara magana kamar zai fashe da kuka "dear Nagode, Nagode, Nagode sosai Allah ya saka miki da mafificin alkhairi, kin bani farincikin da ban taɓa zaton Akwai koda rabin shiba cikin duniyar nan, yanzu kuma ga wani, dama ashe little Aayaan ɗin mu yana raye?" Ɗaga hannuwanshi yayi sama tare da cewa "ya Allah Nagode, Alhamdulillah ala Ni'imatullah," sauke hannuwanshi yayi yana kallon Dr Uthman wanda Fuskarshi ke kunshe da wadataccen murmushin taya abokinshi murna. "Old friend murnar ta isa haka, pls a ɗauki madam aje a cigaba da kula da ita, Nasan kasan duka Abinda Ya dace, so kaga ba saina ɓata bakina ba" "Hmmm Nagode Uthman! Agaida min da Madam da mama, kace in'sha Allah zan shigo na gaisheta," ƙarasawa yayi gurin Nawaz be jira komai ba ya sunkuci kayarshi yayi waje rungume da ita, ko a cikin motar ma rabin jikinta na cikin jikinshi. Kasancewar itama Nawaz ɗin ba daɗin jikinta take ji ba saboda ga jirin har Yanzu be sake taba, ga heartburn da faduwar gaba, sai hakan yasa batada wani karsashi, shiyasa ma ta zubawa Aayaan ɗin idanu yake Abinda yaga dama. A motar ma be barta ta huta ba, sai lissafo mata abubuwa yakeyi yana cewa zataci, sai dai ta girgiza mishi kai alamun a'a. Da taga bafa zaiyi shiru ba saita yanke shi da cewa "kaza zanci da yoghurt da ice cream sai kilishi" Jin tayi magana sai yaji kamar an mishi bushara da gidan Aljannah, sauri ya ƙara don ya isa restaurant ɗin da yake ganin ya dace da abubuwan da yake da bukata. Da kyar ya fita ya barta ita kadai a cikin motar, shi a nashi da akwai hali goyata zaiyi ya tafi da ita, cikin ƙasa da minti goma sai gashi riƙe da manya manyan shopping bags guda uku, back seat ya zuba su sannan ya shiga driver side ya cigaba da tuƙi, Allah Allah yake su isa gida domin yaba Mummy da Aseey Labarin ashe little Aayaan Yana nan. Dakyar yayi parking ɗin motar sanda suka iso gidan tsabar zumudi, buɗe gefenta yayi ya sunkuceta duk uban Mutanen dake cike a harabar gidan be damu ba, cikin usulin main falour ya nufa ɗauke da ita, wasu dasu kasan Abinda Ya faru ne suka fara tambayar shi "ya mai jiki?" "Da sauƙi" yana ci gaba da durfafar faloun, cikin Sa'a kuwa babu wasu mutane masu yawa, mummy ce sai Aseey sai muhsien sai Colonel da wata kanwar marigayiyar da yayar Colonel, sai wata Yar dattijuwa wadda ba yace wacece ba. Yana karasa shiga ya kwantar da Nawaz a saman three sitters sofa dake facing ɗin Mummy, gyarata yayi sai kace wanda ya kwantar da jinjiri yana tsoron kada ya fado ƙasa "Mum and Dad please ku tayani murna" Sosai sunan da Aayaan ya kirasu dashi ya dake su, Colonel addu'a ya hau yi a cikin zuciyarshi kan Allah ya tabbatar da hakan, ita kuma Mummy ji tayi zuciyarta na bugawa da sauri da sauri, Cikin rashin Sa'a kowa ya saci kallon kowa ai ko sai suka haɗa ido, da sauri Mummy ta kauda kanta Saboda wani kwarjini da taga idanun colonel sunyi mata. "Son bakada hankali ne anyi rasuwa ko uku ba'a yiba zakazo kana cewa a taya ka murna?" Cewar Mummy Wadda ta faɗa da biyu ne, tana nufin kada ma colonel ya soma tunkarar ta da wani zancen yana sonta zai aureta. Ile kuwa sakon ya isa inda takeso, aikam colonel na gane cewa dashi take sai yayi saurin cewa "Ai mutuwar wani tashin wani, yanzu dan anyi rasuwa shi kuma sai ya rufewa kanshi kofar farin ciki? Ta riga ta mutu Kuma ba zata dawo ba, Abin da ya rage Yanzu tsakanin mu da ita shine addu'a da fatan alkhairi da dace da kyakkyawan makwanci." Tsaff mummy ta gane shima ya rama ne, sai ta ƙasa cewa komai illah "Allah ya jikanta yayi mata Rahma" "AMEEN'' duka suka furta, "Son meya faru?" "Dad cikin jikin sweetheart yananan ashe" Mikewa tsaye Aseey tayi wadda tuntuni take zaune amma bata furta koda a ba. Ina ji yiwa kowa Fatan Alkhairi MATAR Rasheed ❤️....*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *88* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* With high excitement tace "bro da gaske cikin yananan?" Gyaɗa mata kai Aayaan yayi haɗe da ɗaga mata gira, Kamar zata faɗi don sauri haka ta ƙarasa gaban Nawaz tana yi mata magana ƙasa ƙasa daga bisani kuma ta fita daga faloun. "Allahamdulillah ala Ni'imatuka ya Rahman" Abinda Colonel yace kenan fuskarshi cike da matsanancin farinciki. Itama mummy saida ta kasa boye farincikin ta duk da bata furta komai ba a matsayin ta na suruka, amma daga kalle ta zaka gane tana cikin farin ciki, suma sauran mutanen gurin Sosai suka nuna farincikin su duk da basusan usulin Abinda ya faru a baya ba. Ita dai Nawaz Duk kunya ta cikata, yanzu kowa yasan ciki gareta bayan kuma kowa yasan Abinda ke faruwa kafin ayi cikin, daɗa rintse ido tayi tana tasbihi Acikin zuciyarta, tunda akace cikin nanan bataji wani Abu game dashi ba sai yanzu, ji tayi dama zata iya ganin waye a cikin nata, amma tasan in'sha Allah mai Albarka ne tunda Allah ya kareshi daga lalacewa. Aayaan ne ya karaso ya ɗauketa yana fita daga faloun zuwa dakinsu, Babu wanda ya dube shi balle ya tanka mishi tunda sun riga da sun gama gane halinshi (baya iya boye soyayya ga wanda yake so) Saida ya tabbatar ya kwantar da ita sannan ya fita don ya koma mota ya dauko abubuwan daya siyan mata a hanya. Naufal ne tare da fudail suka shigo Harabar gidan, alamun kamar daga kasuwa suka dawo hannunsu ɗauke da manya manyan bamboona, tsabar farin cikin da yake ciki yasa be tuna cewa basusan komai game da cikin ba ya tare su yana cewa "My twins kunsan da mukaje asibiti Ashe cikin be zube ba!" "Cikin wa?" Cewar Naufal yana shafa kai alumun tunani "Au ashefa baku saniba ba " cewar Aayaan sannan ya ƙara da cewa "dama kwanaki ne mu dear tayi ɓari, to ashe cikin nanan be zube ba sai dazu da mukaje asibiti akayi mata scanning da wasu tests akace yana nan. Cikin nuna farin ciki afili Naufal yace "masha Allah, Alhamdulillah, Gaskiya naji daɗi, nima zanyi ƙani, idan kuwa mace ce nayi mata wallahi" Ajiye bamboon Fudail yayi tare da cewa "to sannu ɗan iya, daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zaƙi! To idan namiji ne kayi aboki idan kuma mace ce nayi Mata" Dariya Abin yaba Aayaan, "to to to ya isa haka, bari naje nabar auntyn taku ita kadai" "Okay Uncle sai mun hadu anjima" cewar Naufal yana ballawa Fudail hararara, nanfa musu yaci gaba, shidai Aayaan yayi saurin barin wajen bayan yasa hannu a cikin ɗaya daga cikin shopping bag din ya ciro babban plastic take away guda ɗaya ya mikawa Naufal tare da cewa "for both of you, kuma saura kuyi faɗa! Nasan halinku" °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Anan wajen fauziyyah ta zube a ƙasa tana rusa ihu, Abinda taketa gudu kenan shi yasa koda yaushe takan cewa umma ta riƙa haƙuri akan wasu abubuwan amma taƙi, har gurin bokayen ƙarya ta riƙa kaita don dai taga babu Abinda ke samun su ummin Nawaz kila ta haƙura amma ta ƙi denawa, kullum ƙiyayyar gaba takeyi, itama saida tayi iya kokarinta wajen dasa mata ƙin Nawaz ɗin. Yanzu fisbilillah kamar ita ace babanta ya saki mamanta? Ai wannan ma babban abin gori ne Wallahi, ga mazan yanzu da Neman ba'asi, Abinda be kai ya Kawo Bama sai suyi maka gori akai, balle Abu irin wannan, barin yanzu ita kanta auren nata girgiɗi yakeyi. Inna talatu ce ta kama ta ta miƙar da ita tsaye tana bata baki "Addu'a zakiyi fauziyyah ba kuka ba, domin kowa da Irin tashi kaddarar, fatan mu kawai shine Allah yasa muyi kyakykyawan ƙarshe, kuma wannan kukan da kikeyi ƙara tayar mata da hankali zaiyi. Jamila kuwa ji takeyi kamar ƙasa ta tsage ta shige ciki saboda kunya da dana sani wadda take ƙeya ce, tuna abubuwan da suka faru a baya ta fara yi, lallai umma itama tanada laifi, domin sanda Nawaz ta fara ganinta ta wanda ya banka mata cikin dake jikin ta saida tayi mata magana akan ta dena kulashi saboda kawarta tace mata ba mutumin arziƙi bane, amma umma tace mata ta rabu da ita baƙin ciki takeyi mata saboda ita ba'a zuwa wajen ta, gashi kuwa yanzu ta tabbatar da gaskiyar Nawaz tunda ya haɗa ta da ribar kwaɗayi ya gudu ya bar ta tana ta fama da wahala da kunya da nadama. Allah sarki, shiyasa hausawa ke cewa kayi mai kyau zakaga sakamako, idan ma ranka bekai ba duniya zata shaida, yanzu babu Nawaz amma Jamila ta tuna cewa taso ta hana rayuwar ta shiga tasgaron da take ciki a yanzu, a yanda takeji ma da zata mutu Lokacin naƙuda da taso hakan. ummi kuwa bin bayan abban Nawaz tayi tana tunanin ta inda zata bullowa maganar. Babu irin bugun kofar da ummi bata yiba amma shiru ko motsin shi taki ji balle tayi tunanin zai buɗe, haka nan ta juyo ta dawo jiki a sanyaye, a cikin ɗakin umma ta tarar dasu duka suna zaune, jamila da fauziyyah sunata jan majina, umma kuma kuka takeyi bilhakki, tana ganin shigowar ummin Nawaz cikin ɗakin tayi saurin haɗe hannuwanta guri ɗaya "Rahma don darajar Alqur'ani ki yafe min, kila dalilin haka na samu wani sauƙi a cikin hukuncin da Allah zai yanke min" "Umma nifa tun tuni na yafe miki, sannan ki dena cire rai da rahmar Allah Domin shi me yafiya ne kuma yana son masu tuba idan sun yi laifi'' "Kaico na!! Dama ace nice me wannan kyakykyawar zuciyar da bata rama sharri da sharri, Rahma kin tsira, kin tsira!" Cewar umma tana kaɗa kai cikin ciwo da tsantsar nadama. Inna talatu ce tace "Naji daɗi da Allah yasa kika gane kuskurenki tun kafin lokaci ya ƙure miki, yanzu abinda ya rage miki shine kiyi tabbatacciyar tuba me cike da nadama, sannan kisa a ranki cewa bazaki kuma yin wani abu makamancin abubuwan da kika yi a baya ba, to In'sha Allah sai kiga Allah ya yafe miki" Jinjina kai Umma tayi Sannan tace " yanzu talatu kece kike bani shawara akan yadda zanyi Allah ya yafe Min bayan irin muguwar tsanar danayi miki ba tare da kinyi Min komai ba?, Lallai ZUCIYA KOWA DA IRIN TASA" "Umma kenan! Ai kowa da Irin tashi kaddarar, kawai dai abar maganar domin komai ya wuce in'sha Allah" Ummin Nawaz ce takai dubanta ga jamila daketa risgar kuka bilhakki, ita kuma fauziyyah ta cure guri ɗaya da alamun kukan zuci takeyi wanda yafi na fili illata gangar jiki da ruhi da kuma jidata zuciya, "Jamila ku bar kukan nan haka mana, addu'a ya kamata ku riƙa yi a cikin zuciyarku sai Allah yasa kuji sanyi a ranku" *Jama'a yau dai dubun umma ta cika* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Koda Aayaan ya koma ɗakin sai ya tarar har Nawaz ɗin tayi barci, zama yayi ya zuba mata idanu yana kallonta. Murmushi ne ya kufce mishi sanda ya lura da irin haske da taushin da fatarta ta ƙara, Lallai shima ya tafka shirme! Ya kamata ace ya lura da chanzawar da jikinta yayi a Matsayin shi na likita, koda dai ba yarda takeyi dashi sosai ba. Cikin barcin Nawaz ta juya alamun barcin nayi mata daɗi zata gyara kwanciya, da sauri Aayaan ya kwanta a gefen ta take ƙoƙarin juyawa, tsaff ta shige cikin jikinshi ta cure kamar kwanciyar jinjiri a cikin mahaifa. Murmushi kawai Aayaan yayi, wai yau shine cikinshi ke jikin Nawaz? Shine zai zama uba nan da wani ɗan Lokaci, ya rasa me yasa duk sanda yaga sauyi a cikin rayuwarshi saiya tuna *sanda ya fara ganin Nawaz a cikin daji wajen ƙarfe biyu da rabi na dare nannaɗe cikin zanin gado.* Samun kanshi yayi da shafa gefen fuskarta sannan ya furta "I Love You Madinah" a fili. Ta chan gurin su mummy kuwa Aayaan na fita itama ta miƙe ta nufi masaukinsu domin ita zaman gidan ma ya fara isarta yanzu, har ta kosa ayi Bakwai su koma nasu gidan, kuma ba Komai bane sanadi sai Colonel daya ke ƙoƙarin karya mata zuciya. Tana tashi kuwa colonel ya kalli Wadda tafi kowa tsufa a gurin yace goggo zuwa injima inaso muyi magana in'sha Allah" "Kada ka damu ɗan lele, Allah ya kaimu anjimar lafiya" Sauran ne suka amsa da "Ameen Allah ya amsa" Murmushi kanwar marigayiyar tayi tare dayin gyaran murya Alamun zatayi magana me ɗan muhimmanci, sai hankalin kowa ya koma kanta "Ni kuwa yaya soja (haka Yawancin dangin shi suke ce mishi) me zai hana ka auri wannan balarabiyar, tunda kaga itama batada Aure kuma kaima yanzu ga taka kaddarar! Ni a ganina gara kuyi Auren sai ya zama duka an haɗu an zama dunƙulallen iyali da ayita zama a rarrabe" Charaf yayar Colonel tace "Wallahi Nima naga sunyi mugun dacewa, kuma koba haka ba naga akwai sabo sosai tsakanin ta dasu Fudail, sannan shima naga ya saba da nata yaran sosai, kunga ko iya haka ma zai alamta mana cewa za'a yi zaman lafiya idan an haɗu waje ɗaya domin kowa yanason kowa." Jinjina kai goggo tayi haɗe da cewa "tabbas wannan shawara ce me kyau duk da Ni naga alamar ba Lallai ita balarabiyar ta yarda ba" "Amma goggo me yasa?" Kanwar marigayiyar tace "Ni dai a nawa tunanin ne naga Kamar ba zata yarda ba" cewar goggo tana gyara mayafinta daya zame daga kanta. Duk maganar nan da sukeyi Mummy na bakin kofa tana jinsu saboda ta dawo ta ɗauki muhsien da yayi barci a kujera, Jinjina kai mummy tayi "lallai kuwa dole nabar gidan nan tun kafin a kira mini ruwa *Ni ko matar Rasheed nace ai an riga da an kira miki ruwan* Kamar ta koma ɗaki sai kawai tayi shahada ta shiga da sallama, duk sai suka bita da Kallo suna nazarin maganar da goggo ta gama yi Yanzu, shi kuma colonel ji yake kamar ya ɗauketa su tafi inda babu kowa su zauna, amma ina babu hali. Wani irin kyau ta ƙara mishi sosai, babu wanda zai kalleta yace ita ta haifi Aayaan balle kuma Aseey, irin madaidaicin jiki gareta me kyau kuma ya haɗu da tana kula dashi, koda yaushe zaka sameta da jan lalle kuma fatar nan tata kullum a gyare.. Ko yanzu ma haka take kamar amaryar Maiduguri, domin ta nannaɗe jikinta cikin jan lafaya dukda ba kwalliya tayi ba saboda a gidan rasuwa take kuma mutuwar ta taɓa ta sosai, amma a haka idan ka ganta zaka zata kwalliya tayi sai dai idan ka lura da kyau zakaga damuwa kwance saman fuskarta. A tare suka amsa mata sallamar kamar haɗin baki, duk saita ji ta wani iri, har takejin dama komawa tayi bata shigo ɗakin ba. "Sannunku goggo! Na dawo na ɗauki muhsien ne" "Allah Sarki! Ki bari ɗan lele yakai miki shi naga kamar ba daɗin jikinki kike ji ba?" Da sauri Colonel ya miƙe ya sunkuci muhsien tun Kafin yaji amsar da zata ba goggo. Itafa Abin nan ya fara isarta, wai ya za'ayi gotai gotai da ita har da jikoki a riƙa ƙoƙarin yi mata auren dole? Sai kawai ta juya ta fita ba tare data ce komai ba, da sauri colonel yabi bayanta shima. A dai dai corner ɗin kitchen sukaci karo da Aseey riƙe da manyan warmers guda biyu, shiru tayi tana kallonsu, domin ganin colonel tayi ya juye kamar daddyn ta sak, ji tayi dama Kawai su zama ma'aurata kila ma Mummyn nata ta samu sauƙin ƙuncin da take ciki na wasu abubuwa da yawa. Colonel ne yace "daughter me aka samar mana ne haka?" Murmushi tayi "Daddy cous cous na dafawa sis Nawaz nasan zataji daɗin shi, shine na tuna da kai nace bari kaima na dafa maka na neman Albarka, kuma ko Daddy the funny facts shine nayi amfani da method ɗin mummy ne yadda takeyi mana tace a Sudan haka sukeyi" "Wow wow!!! masha Allah kice daɗin shi ma na musamman ne, bari na raka mummy na dawo sai nazo muci" "Mummy kuwa data zama kamar gunki a tsaye ji tayi kamar ta rufe Aseey ta duka, meyasa taza sakata a cikin abinsu bayan ita ba tankasu tayi ba. Fuu haka ta wuce su tabar gun, ba tare data kuma ko kallon inda suke ba.. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Sai bayan kamar awa uku Abban Nawaz ya buɗe Kofar ya fito, ɗaga labulen ɗakin umma yayi tare da cewa "kizo ki wuce ki fitar min daga gida, kuma ki tabbatar kin ɗauki jamila kun tafi tare, sannan koda wasa kada ki sake na kuma ganinki ko a Kofar gidan nan ne. fadin irin tashin hankalin da suka shiga duka ma kamar ɓata baki ne, kada ma jamila taji labari, nan take ta fara murkususu tana cije baki, kafin wasu mintoci jini ya fara malama daga gurin da take zaune yana gangarawa, ita kuwa fauziyya neman numfashin ta tayi ta rasa, ai kuwa da gudu inna talatu tayi kan jamila ita kuma Ummi tayi gun fauziyyah... *NOVEL YAZO GANGANGARA, 08093215055 GA NUMBER TA GA MAI BUKATAR ZUMUNCI, GYARA KO SHAWARA (WHATSAPP KAWAI) NAGODE* *Matar Rasheed ❤️**🎀 🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *89* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Sakin labulen ɗakin Abban Nawaz yayi ba tare da ya damu da halin da yaga su Jamila ba, Domin yanzu duk wani abu da ya shafi Umma baƙinshi yake gani. Cikin ikon Allah ummin Nawaz ta samu fauziyyah ta farfaɗo dakyar, Ruwa ta bata tasha sannan ta koma gurin jamila inda inna talatu ke tunanin sai anje asibiti Domin dukkan alamu sun nuna naƙuda takeyi kuma gashi cikin be isa haihuwa ba. "Inaga fa sai anje an taro adaidaita mu kaita asibiti kada wani abun ya faru, saboda jinin da yawa yake zuba gashi ta fara fita daga hayyacinta" "To bari na samo" cewar ummin Nawaz tare da hanzarin fita daga ɗakin "Kada ki sake ki fita daga cikin gidan nan" Suka jiyo muryar Abban Nawaz a kausashe. A zuwa wannan lokacin zuciyar umma ta gama bushewa gaba ɗaya, jira kawai take taji ance mata Jamila ta mutu, tana inda take a zaune domin babu ƙafa kuma koda da kafar bata tunanin zata iya tashi saboda tashin hankalin da take ciki, hannuwanta kawai tasa ta rufe fuskarta tana jero istigfari a cikin zuciyarta. Tsaye ummin Nawaz tayi tana ta'ajibin wai ya akayi Muhammad ɗinta ya zama haka ne? shirin bashi haƙuri takeyi saboda kada wani abu ya sameta. "Abban Nawaz don Allah kayi haƙ....." "Sanda tayi cikin tayi shawara dake ne da yanzu kike nemar mata mafita?" Maganar data ƙara dukan Jamila kenan jikin nata ya ƙara rikicewa.. Itama Inna talatu sai ta fito da nufin su haɗu su ƙara bashi haƙuri kila ya sauya ra'ayinsa, kafin ta ƙarasa gurin da suke tsaye ma ya shige ɗaki ya turo ƙofa. Cirko cirko sukayi a bakin kofar suna tunanin mafita, "Rahma kinada garin kanumfari da garin Cinnamon" Inna talatu ta tambayi ummin Nawaz "Eh inada su" ummin Nawaz tace tare da nufar falonta don daukowa "Ki haɗo da sabuwar reza nasan bakya rabo da ajiyewa" inna talatu tace da ƙarfi yadda ummin zata jiyota Da sauri ta fito riƙe dasu har tana neman yin tuntuɓe tsabar tashin hankali. A inda suka barta Anan suka sameta, gaba ɗaya jikinta yayi laushi, "Umma inaga fa sai dai muyi mata dabaru irin namu na gargajiya don inba haka ba zamu iya rasa ta" inna talatu tace tana ayiye hijabinta a gefe "Kuyi mana, Allah ya taimaka" Abinda umma ta iya cewa kenan ta maida hannunta ta rufe fuskarta. Kofi ummi ta dauko ta ɗebo ruwan dumi ta kawowa Inna talatu, amsa tayi ta juye Garin kanumfarin da na Cinnamon ɗin ta jujjuya saboda ya jiƙu da wuri. Fita ummi tayi ta ɗauko muciya a kitchen saboda itama zasu bukace ta, dago kan jamila tayi ta kafa mata kofin a baki tare da cewa sha. Tsabar azabar da jamilan take ciki yasa bata ji daci da yajin kanumfarin ba ta riƙa kwankwanɗa har Saida ta shanye shi tass, jira sukayi na Tsawon minti goma amma shiru babu wani yunkurin tawowar ɗa daga cikin. Ummi ce ta mikawa Inna talatu muchiyar tace "inaga fa sai anyi amfani da muciya kada karfinta ya gama ƙarewa, buɗe bakin jamilan ummin Nawaz tayi ita kuma Inna talatu ta tura mata muciyar chan cikin makogoronta, cikin ikon Allah kakarin da tayi sai ta fara yunkuri, bata cire muciyar ba saima ta ƙara turawa ciki yadda za'a samu tayi yunkurin mai karfi. Allah ya taimaka har jinjirin ya fara tawowa, gyara kafafuwanta ummi tayi don ta duba taga ko jikin nata ya buɗe, amma cikin rashin Sa'a ɗan ya sako kai har ana ganin gashin kanshi amma jikin a tsuke yaƙi buɗewa. Da sauri ummi ta fita zuwa dakinta ta ɗauko man zaitun da man kwakwa, sosai take zubawa tare dasa hannunta tana bude cikin jikin jamilan ko Allah yasa yaji santsin man ya buɗe, amma ko gezau yaƙi buɗewa, babu yadda basuyiba amma abu yaci tura. "Ina rezar nan take" inna talatu ta tambayi ummin Nawaz Miƙa mata rezar ummin Nawaz tayi tana jin zuciyarta na karyewa saboda tasan yanka ta talatu zatayi tunda ta kasa haihuwar da kanta, Aikuwa dai abu babu daɗi saida ta ƙara ta har guri biyu sannan aka samu kan ɗan ya fito, cikin dabara suka taimaka jinjirin ya gama fitowa.. Saida ya gama fitowa suka lura baya numfashi, gashi dama ɗan karami ne sosai, jijjigashi suka riƙa yi ko suma yayi amma daga baya sai suka gane ya mutu ne, wato wahalar da yasha a ciki yasa ya mutu kafin a haifeshi. Inna talatu ce taciro mahaifa tare da kwashe mata jinin cikin marar ta sannan tasa wani zani ta tare jikin jamilan dashi, ko motsi kwakkwara ta kasa illa idonta da yake abude ne kawai zai shaida maka tana raye bata mutu ba. Shirun fauziyyah ne suka ga yayi yawa, koda ummi ta ƙarasa kusa da Ita ta duba sai taga ashe ta kuma sumewa ne, cikin tashin hankali ta fita ta ɗebo ruwa ta fara yayyaafa mata.... *(Jama'a kun dai ga Yadda jamila tasha wuya, yau da ace Aure tayi ta samu cikin, ana farin ciki za'a kaita asibiti kuma ayita nan nan da ita, kowa yana cikin tashin hankali har saita haihu, ballantana ma mijinta, idan yanada hali ma har kyauta zaiyi mata bayan ƙaunarta da zai kara, ga abinci me kyau da gina jiki da za'a tanadar mata tun sanda ta samu cikin ta yadda idan tazo haihuwar Allah zai taimaka naƙudar tazo mata da sauƙi)* *ALLAH KASA MUFI ƘARFIN ZUCIYAR MU, KUMA ALLAH KA ƘARA NESANTAMU DAGA KAIDIN SHAIDAN DA SHARRINSA (AMEEN)* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Bin bayanta colonel yayi, koda ya shiga ɗakin be ganta ba sai kawai ya kwantar da muhsin ɗin yaja musu Kofar ya fito ya koma falon. Anan ya samu Aseey zaune a dining tana jiranshi, ta fara serving dinshi kenan saiga su Naufal sun fito kowa da rabin ƙatuwar kaza a hannunsa yana yaga "ina kuka samo kaza ƴan-biyu" goggo ta tambayesu miyaun ta yana tsinkewa "Yaya Captain ne ya bamu" Naufal yace yana ƙarasawa dining din shima. Kafin yace wani abuu tuni muryar Fudail ta karaɗe ɗakin "Aunty pls Nima a zuba kin better ɗin da aka haɗawa Daddy" "Kaji ɗan baƙin ciki" abinda Naufal yace kenan yana balla mishi harara "wato saboda kaga na riga ka shine zaka yimin katsalandan Koh" Daddy ne yace "kuci gaba kunsan sauran ai, tunda ku ako ina kuma a gaban kowa ma saikun raba hali" Shiru duka sukayi ba tare dasun shirya ba Goggo ce tace "wai Ni kam gidan nan sai naga yana komawa kamar ba gidan zaman makoki ba" "Eh goggo ai kinsan idan mutum ya daɗe yana jinya mutuwarshi bata cika damun Mutane ba kamar wanda ana tare da an rabu ace wane ya mutu" cewar kanwar marigayiyar "Ai kuwa dai ai Aunty tasha jinya wallahi, Allah dai ya jikanta yasa kankarar zunubai ne" cewar yayar Colonel tana miƙewa °°°°° Sosai Nawaz tayi barci domin sai bayan la'asar ta tashi, samun kanta tayi rungume cikin jikin Aayaan shima yana barcin shi peacefully. Motsin data yine ya tashi Aayaan, da sauri ya tashi ya zauna tare da cewa "sweetheart kin tashi? Ya jikin naki? Fatan babu inda yake miki ciwo Koh?" Ɗaga mishi kai tayi kawai domin bata sanma tambayar da zata amsa mishi ba, Ɗaukar ta yayi ya kaita bathroom ya wanke mata baki shima ya wanke nashi sannan ya dawo da ita ya zaunar da ita a saman bed. Duka abubuwan daya siyo mata ya buɗe mata tare da cewa "Ranki ya daɗe Bismillah!. Sosai take cin kazar kamar ɗan gudun hijrar daga fi sati be ga abinci ba, tana gama ci zata sha madara sai amai ya kwace mata, tashi tayi da gudu da nufin ta shiga bayi amma Aayaan yayi saurin riƙe ta tare da rungumeta "dear kiyi anan kawai.. Tun kafin ya ƙarasa tuni aman ya tunkuɗo waje, duk jikin Aayaan ɗin ya ɓaci har wajejen wuyanshi, sam shi ba wannan bane ma ya dameshi illa yunƙurin da yaga tana ƙara yi, sai faman jera mata sannu yakeyi kamar wadda za'a shiga da ita ɗakin haihuwa.. *MASU KARATU KO A IYA NAN AI MUNGA ILLAR SON ZUCIYA, JUST KU KWATANTA JAMILA DA WAHALAR DA TASHA, NAN KUMA GA NAWAZ DA YADDA AAYAAN KE KULA DA ITA* MATAR RASHEED ✍️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *90* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Duk ya rude sai sannu yakeyi mata, saida ya samu ta gama duka aman sannan ya kwantar da kanta a ɗaya gefen kafadar shi inda be ɓaci ba, bayanta ya riƙa shafawa a hankali soboda tayi saurin samun relief. "I'm sorry sweetheart, wallahi na kasa riƙe aman ne Kum...... "Shiii🤫 keep quiet, meye zaki bani haƙuri bayan Nine nayi cikin! Kuma after that aini zaki haifawa yaro and kuma ma aike kika sha wahala baniba, so Kinga ai Ni ya kamata na baki hakuri!! I'm sorry dear duk Nasan nine naja miki duka wahalar nan, da ace banyi cikin ba da yanzu kina sabgarki cike da lafiya" Mamaki ne yasa Nawaz tayi shiru tana sauraron shi batare data ce komai ba har ya gama maganar shi, "wai wane irin miji Allah ya haɗa Ni dashi ne? Wasu mazan fa sun san su sukayi cikin amma kyamar ka suke komawa suna yi, wasu har ma su riƙa kyarar ka suna daka maka tsawa idan kayi wani abun, Lallai Allah ya zaɓe ta a cikin dubu" zancen da Nawaz ta gama ayyana wa kenan a cikin zuciyarta. "Sweetheart bakice komai ba! Hope ba fushi kike dani ba!" Duk maganar da Aayaan zaiyi sai taga kamar ƙara kwance mata notikan mamaki yake ƙara yi, "No dear, ni baka yimin komai ba, kuma ai dama burin kowace mace ta zama uwa. So kaga babu wani laifi daka yimin" Ɗaukar ta yayi ya shiga bathroom inda ya gyara mata jiki sannan yayi mata wanna shima yayi suka fito. Zaman ɗakin duk sai ya ishi Nawaz duk motsi saiya ce menene? Me yake damunta? Ko akwai abinda take bukata? Tafiya ma ya hanata yi sai dai komai ya ɗauke ta, hatta bayi idan zata shiga saiya rakata. "Sweetheart pls kabarni mana! Meyasa zaka riƙa wahalar da kanka haka ne?" Dariya Aayaan yayi "lallai har yanzu akwai sauran shakkun dakikeyi akaina game da soyayyar ki kenan Koh?" "A'a sweetheart" "Hmmm to meyasa kike cewa na rabu dake" "To shikenan kaci gaba! Nagode" cewar Nawaz tana kwantawa a saman jikinshi °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Kafin wani lokaci Inna talatu da ummi sun gyara ko ina tass kamar ba inda aka haihu ba, ko ƙarni babu illah kamshi da ko ina keyi, gefe ɗaya kuma Fauziyya ce kwance ana ƙara mata ruwa. Likitan ce tace "a buɗe jikin Jamila ta gani saboda tasan me zata dauko wanda zatayi amfani dashi wajen yin ɗinkin, koda ta duba sai ta girgiza kai kawai ta fita. Inna talatu ce ta kalli ummi tace "Rahma ko na kira Khalifa na basu yaron nan suje su birne shi? Kinga har yanzu Abban Nawaz be fito ba kuma ga yamma ta fara yi" "Ki tambayi umma kiji" abinda ummin Nawaz tace kenan saboda bataso ace ta cika zaƙewa a abun. Kafin ma Inna talatu ta tambayeta Umma tayi saurin cewa "duk abinda ya dace kuyi, aini babu abinda zance muku domin kun nuna min ku ƴan halal ne, kuma ai Jamila ƴar kuce" Waya ta ɗaga ta kirashi tare da cewa yazo bakin junction ya sameta. Ba'a fi minti goma ba ya kira yace ya karaso saboda dama yana kusa da gurin. Nannaɗe jinjirin tayi cikin fallen zani ta tallabeshi a cikin hijab dinta ta fita, a tsaye ta sameshi bakin wata kwata, "yauwa Khalifa don Allah so nake ka samu abokan ka ku ɗan binne Yaron nan, wata yarinyar kawata ce tayi ɓari, kuma ba'a nan garin suke ba sunzo ne" "Haba inna ai babu komai kin wuce nan, amsar shi yayi ya wuce ya tafi tare da ciro wayarshi a cikin aljihu don kiran sauran abokanshi saboda asamu wanda zai siyo likkafani da sauri. Koda inna ta koma ta tarar likitan ta dawo harta yiwa jamilan allurar kashe zugi data barci, likitar yare ce shiyasa basu damuba domin sunsan maganar bazata fita waje ba tunda ba sanin su tayi ba. Shiyasa ma sanda inna talatu taje Asibitin don samun likitar da zata biyota gida tace a bata yare, tunda su ba kasafai suka cika magana ba. Kuma basaso su fito da jamila kada asan halin da suke ciki. A natse take aikinta, tsaff tayi ɗinkin ta gama sannan ta ƙara yi mata wasu allurorin sannan ta rubuta wasu magunguna tace a siyo mata ta shasu na tsawon sati Daya. Duk wani kudin da ake buƙata ummin Nawaz ce ta biya. Saida taga komai ya kankama sannan ta tashi ta nufi ɗakin da Abban Nawaz ya shiga domin ayita ta ƙare Koda ta shiga a kwance ta ganshi yayi nisa cikin tunani, zama tayi gefen shi tare da taɓa shi kaɗan. Firgigit ya dawo hayyacinsa tare dayi mata murmushi, itama murmushin ta mayar mishi tare da cewa "Akwai abinda kake bukata ne? Inaso zamuyi magana Don Allah" "Bana buƙatar komai tauraruwata, sai dai ina fatan sun fita sun bar min gidana " Ƙasa da murya ummin Nawaz tayi tana tausar zuciyarshi akan yayi hakuri don Allah, ita bazata so ace ya rabu da umma ba Saboda tayi mata wani Abu ba, ai ko babu komai itace Uwar gidansa Hutsancewa Abban Nawaz yayi akan ta rabu dashi, domin shi abinda yayi shine dai dai kuma bazai taba nadamar yin hakan ba. Saida aka kai ruwa rana tukuna ya Yadda da cewa umma ta zauna tayi idda a cikin gidan,idan ta gama saita tafi. Ita kuma ummin Nawaz tayi hakan ne saboda ta samu isasshen lokacin da zata kira baffansa ta faɗa mishi Abinda ke faruwa. *Kamar yadda iska ke kadawa haka lokaci ke gudu yana wucewa dakiƙa bayan dakiƙa, Sa'a bayan Sa'a, kwana bayan kwana, sosai komai ke chanzawa wani ya canza mana da Alkhairi wani akasin haka, wani ya bamu abinda muke so wani ya karbe mana.* Yau su Mummy ke shirye-shiryen komawa gida domin har anyi Bakwai ɗin matar colonel, kuma duk iya zaman da sukayi Mummy taƙi ba colonel wata dama samm. Ita kuma Nawaz abu ya isheta domin sam bata komai sai barci, hatta da abinci Aayaan baya bari taci da kanta sai ya bata. Ga mummy da Aunty Aseey a gefe, suma su Naufal da fudail ba'a barsu a baya ba saboda ko fita sukayi sukaga mai kayan marmari sai sun siyo mata. Ganin fa da gaske tafiya zasuyi yasa colonel ya kira Aayaan gefe "son nidai bazan gajiya ba, don Allah akan dai maganar nan ce da mummyn ku bata so, nayi iya kokarina amma taƙi bani wata dama, Wallahi Ni harna fara karaya domin dama cewa takeyi bazata Aure niba saboda kawarta, to yanzu saboda meye bazata Aure niba? Ko dai nine bata so" "I'm sorry sir, pls kada kace haka, yanzu Abinda nake tunani guda ɗaya ne kawai, idan mun koma gida zanje na samu baffa (kakan Aayaan, wato baban mahaifinsa) na faɗa mishi Abinda ke faruwa, to nasan hardai naje gurinshi to ka ajiye anyi Auren ka da Mummy an gama in'sha Allah," Godiya sosai colonel ya rinƙa yiwa Aayaan Kamar zaiyi kuka, har Saida Aayaan yaji duk kunya ta kamashi me karfi, wato shi yau colonel yakewa godiya kamar zai mishi sujada. Namfa ake yinta domin Fudail da Naufal kame wa sukayi kan cewa sufa sai dai a tafi dasu, babu musu colonel yace "umma ta gaida Aysha" shima dama nemar hanyar dazaije maidugurin yakeyi da wuri, to kuwa idan su Naufal suna chan Babu maiyi mishi shamaki da zuwa, kenan Abin zai zo mishi a saukake. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ta ɓangaren ummin Nawaz kuwa ta samu lokaci ta kira baffa inda tayi mishi bayanin Muhammad ya dawo sannan ga abubuwan da suka faru, sosai yaji daɗin dawowar ɗan nasa sannan yayi Allah wadai da halayen Umma, amma ganin yadda ummin Nawaz ta damu akan don Allah ya sa Abban Nawaz ya maida umma sai yaji jikinshi yayi sanyi. Cewa yayi ta kaiwa Abban Nawaz ɗin wayar, tana zuwa ba tare data faɗa mishi waye ba ta kara mishi wayar a kunne, sallama yayi yana cigaba da sauraro. "Ina so gobe ku tawo maiduguri kaida duka iyalinka" Abinda yaji Muryar mahaifinsa tace kenan. Kallon ummin Nawaz kawai yakeyi "wai meyasa a komai saita yi mishi shigar sauri ne?" Ita dai aje wayar tayi ta fita don zuwa yiwa jamila wanka domin ta juye ruwan, bilhakki take kula da jamila Kamar yadda zata kula da Nawaz hakan yasa cikin lokaci kankani jamilan ta maida jiki sosai kuma ta samu lafiya illah damuwa da tasa kanta a ciki, kuma damuwar tanada nasaba da meye makowar Rayuwar ta anan gaba, me zata cewa wanda zai zama mijinta game da rayuwarta, hakan yasa lokaci zuwa lokaci ummi ke samunfa tana kuka. Itako umma kullum tana Cikin hijabi riƙe da charbi tana istigfari da tuba, mamakin ummin Nawaz kullum baya barin zuciyarta domin kullum cikin hidima take dasu, babu Abinda ta rage illah karawa ma datake yi, kuma haka fauziyyah ma Kusan kullum ummi saita kirata a waya taji ya ƙarfin jikinta. A yanzu ji takeyi da za'a bata Aljannah guda ɗaya ace taba wani kyauta to babu makawa ummin Nawaz zata ba, domin ta rufa mata asiri duniya da lahira. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Su Mummy sun sauka a gida Lafiya, Aseey ce keta hidimar gyara gidan donma anci Sa'a maiyi musu girki ta dawo, miƙewa Nawaz tayi don ta taya Aseey Saboda suyi saurin gamawa, namfa Aayaan ya riƙe ta kan cewa taje ta kwanta wai Little Aayaan yana buƙatar hutu. Ihu ta fara ta nufi ɗakin Mummy "yiiii wayyo, Ni wallahi bazan iya ba" da sauri mummy ta buɗe kofa cikin tarardadi tana tambayar Nawaz cewa meya faru take kuka? "Mummy ni wallahi bansan me yaya Aayaan yake nufi daniba, tunda akace cikin nan yana nan ya hana ni yin komai hatta alwala shi yake min, dana tashi zanyi aiki saiya hanani" "To daughter Yanzu wannan ɗin kikewa kuka?" "Mummy wallahi jikina ciwo yakeyi kuma na gaji da zama" "To yanzu bari zanyi mishi magana ya riƙa bari kina alwalarki da kanki" Tsalle Nawaz tayi "Mummy nifa ba alwala kadai ba harda abubuwa da yawa" Tsallen da Nawaz tayi saida mummy ta jishi a cikin ranta, domin itama a nata gurin matakin da Aayaan ya ɗauka akan Nawaz ɗin yayi mata dai dai, Domin bazata iya jurar rasa cikin a karo na biyu ba, kuma ga Nawaz mayyar aiki ce sam bata gajiya barin ma taji labari akan girki. Lallabata tayi da cewa zatayi wa Aayaan ɗin magana, sai sannan NAWAZ ta wuce ta tafi daki ko kallon inda Aayaan yake bata yiba irin ita ta samu yancin nan. Ɗaukar waya Mummy tayi don ta kira ummin Nawaz daga nan ta kira mummyn sarfraz don taji ya suke, aikuwa murna taƙi barin fuskarta sanda taji cewa gobe su ummin Nawaz zasu sauka a garin kuma ƙarin daɗin shine Abban Nawaz ya dawo. Koda ta kira mummyn sarfraz ta faɗa mata gameda zuwansu ummin Nawaz Maiduguri sai tace itamafa ata bau bau sai taje, yadda ta yanke zance ma shine zata shirya taje gun ummin Nawaz ɗin taji yadda za'a yi tafiyar don tana ganin tare zasu tafi kawai. *Zuwa maiduguri da sukayi ya gyara abubuwa da yawa* *kuma ya haifar da farinciki Sosai a zukatan duka ahalin* Domin Abban Nawaz yaga mijin Nawaz inda take yaji ya shige mishi zuciya, kuma baffa yacewa Abban Nawaz ya maida umma dakinta tunda tayi nadama kuma ya gaggauta yafewa Jamila. Koda Nawaz taga Abban ta haka ta tafi ta faɗa jikinshi ta riƙa kuka har Saida Aayaan yaji kamar yaje ya ɗauketa a gurin. Sosai duka ahalin suka samu kusanci da juna domin a gidan su Aayaan suka sauka duka, sai daga bisani aka zazzaga dangi. Ganin Yadda aka haɗu guri ɗaya yasa Aayaan ya zame ya kira colonel ya shaida mishi cewa yayi sauri yazo yanaga hakansa zai cimma ruwa in'sha Allah. Su kuwa su Naufal da fudail ganin sarfraz da bandi sai ya zama kamar Sallah a gurinsu, duk da cewa su sarfraz ɗin sun girmesu amma suna jin daɗin zama dasu sosai. Hassu kuwa tunda suka haɗu da Nawaz ta like mata, itako Aseey duk murnarta ta koma ciki domin baban Muhsin ya kirata yace ta tabbatar ta koma gida jibi shima yana hanya. Aayaan sanin cewa ga Abinda Ya shirya na Mummy da colonel sai ya sa securities dinsa sukaje suka kwaso kakannin Nawaz na uwa dana uba, sai nashi kakannin na wajen mahaifi, be tsaya nanba saida yayiwa sarfraz kara shima ya kwaso nashi, inda yace kowa ya kira sauran ƴan uwa a shaida musu cewa gobe wajen ƙarfe goma akwai walima a gidan. Aikuwa sosai aka taru inda su Mummy da Aseey suketa mamakin wace walima za'a yi wadda basusan da Ita ba, kuma su basu tanadi komai ba ga mutane sun fara taruwa. Abinda basu saniba shine Aayaan duk ya bada order ɗin duka abinci da snacks da drinks ɗin da za'ayi amfani dasu a kusan restaurant guda Biyar. Gurin ƙarfe tara da rabi kuwa gida duk ya cika da abinci, mutane sai kai komo sukeyi inda gidan yayi tanƙam da mutane daga ɓangaren duka ahalin. Wurin karfe goma da wasu Yan mintuna colonel ya sauka, dakinda su kakanninsu suka yada zango nan Aayaan ya raka colonel. Bayan sun gaisa ne Aayaan yake musu bayanin cewa colonel tun bayan rasuwar abbansu yakeson mummy amma taki bashi dama, ga kuma yanzu Allah yayiwa mai dakinshi rasuwa kuma ya kuma dawowa nanma tace a'a itafa bata yarda ba, Sosai kakan Aayaan ya gyara zamanshi, "to Amma Ayatullah meyasa Ni baka taɓa fadamin ba?" "Ita ta hanamu baffa, ko yanzu ma bata saniba" Shima kakan Nawaz Sosai yayi mamakin wannan karfin halin na mummy, Anan suka yanke hukunci shadaya na bugawa za'a daura Auren colonel da Mummy. Ganin Maganar ta koma ta manya yasa Aayaan yayi sif ya fice ya basu guri, shikuwa Colonel jinshi yake kamar wanda aka ɗauka aka saka a cikin aljanna, shikuwa wace irin Sa'a ya taka yau kuwa? Yanzu wannan dalleliyar balarabiyar ce zata zama mallakin sa? Lallai kuwa ya godewa Allah, kuma shima zaiyi bajinta. Kamar yadda sukace kuwa shadaya na bugawa aka Daura Aure, Mummy na can tana hidima da mutane Aseey ta tawo da gudu tana cewa "mummy! Mummy!! Bakiji abinda naji bane?" "Ooh Aseey Don Allah Ni banji komai ba, ki bari na gama da mutane sai ki faɗa min koma menene " Matsawa kusa da Ita Aseey tayi sosai sannan tace "yanzu fa Naji ana sanarwar an daura auren ki keda daddy colonel, wai ashe abincin bikinki kike rabawa" Tsaye Mummy tayi chak kamar gunki, ji tayi komai na jikinta ya dena aiki...... 😂😂😂😂😂😂😂 Matar Rasheed ❤️*🎀 🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *91* *SECOND TO THE LAST PAGE 😭😭* *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Ko motsa yatsanta ta kasa yi sai zallar gudun da zuciyarta takeyi, wata Irin fargaba ce ta kama ta wadda ko a aurenta na fari bata ji irin taba. "Ashe haka Nawaz taji! Lallai Nawaz nada haƙuri domin ita kanta da ta taɓa aure abin ya bigeta balle wadda bata taɓa aureba kuma bata samma wanda aka aura mata ba" Da kyar ta dawo cikin hayyacinta, ba tare data cewa Aseey komai ba Kawai ta miƙi hanyar sasan da su baffa suka sauka, so take taje taji waye ya shirya mata wannan manaƙisar. Tsabar saurin da takeyi yasa lafayarta ya fara warware wa da kanshi, bata jira komaiba ta ƙarasa cireshi da kanta, Nannaɗe shi tayi ta ɗora a saman kafaɗarta tana ci gaba da tunkarar sashen. Warwarewar da lafayar tayi sai ya ƙara bayyanar da duka surar mummyn a fili, barin ga kuma saurin da takeyi hakan yasa duka jikinta ke juyawa tako ina musamman mazaunta, kuma dama su take ɓoyewa kullum cikin lafayar, sai lafiyayyen gyararran gashinta daya sauka har gadon bayanta. Colonel ne tafe da Aayaan suna maganar yadda za'a bullowa Mummy, basaso taji zancen a bakin wani, sunfi so su faɗa mata da kansu Saboda Abin zaifi zuwan musu da sauƙi. Aayaan ne ya taɓa Colonel yana nuna mishi Mummy Wadda ta nufosu cikin wani irin sauri, "Daddy da Alamu wani yaje ya faɗa wa mummy" Cirko cirko sukayi suna jiran mummy ta karaso gurin su saboda suga yadda za'a kare, abinda basu sani ba shine sam Mummy bata ma gansu ba, gaba ɗaya hankalinta da tunaninta duka yana hanyar kofar ɗakin su baffa. Ganin ta wucesu batace musu komai ne yasa suka gane bata gansu ba, zata ɗaga labulen ɗakin su baffa kenan taji baffa yana cewa "Aini mehtab ta gama yimin komai a Rayuwa, tunda nake da ita ban taɓa yin abu tace baiyi ba, tun Muhammad yana raye ko kara na ajiye bata tsallake wa, kuma har bayan ya mutu bata rage komai daga abubuwan da take yimin ba, Allah dai yayi mata Albarka ya albarkaci Aurensu, yasa shine hanyar da zata shiga Aljannah..... Jin wannan Maganar da baffa yayi akanta sai mummy taji gaba ɗaya gwuiwarta ta sage, bata da wani sauran kwarin gwuiwar zuwa ta samu baffa tace mishi batason auren, juyawa tayi da nufin ta koma daki domin zuwa yanzu ta amince cewa Auren ta da colonel A Rubuce yake. Ganin colonel tayi tsaye shida Aayaan, da alamun ma ba Yanzu suka ganta ba, ji tayi bazata iya cigaba da tsayuwa a gaban suba, wai wannan Abin Kunyar har ina! Fisbilillah ace kamarta ce wai akaiwa auren dole, ta gefen su Colonel ta wuce ba tare data ce musu komai ba. Hakan saiya darsa wa colonel tsoro a cikin zuciyarshi, yaso ace tayi masifa,tayi jaraba Saboda ta fitar da duka damuwar ta, wannan shirun yana nufin Akwai sauran rina a kaba kenan. Da ɗan sassarfa ya ƙarasa kusa da ita tare da ɗan shan gaban ta "Pls ki tsaya ki saurareni, wallahi shirun nan ƙona ni yakeyi, koma me zakice pls kice. Kaucewa tayi zata cigaba da tafiyar ta, besan sanda yasa hannunshi ya riƙe damtsen taba "pls ki saurareni, beat me, slap me or do anything you like, wallahi mehtab da gaske ina sonki, kuma bawai nayi miki karfa karfa bane saboda na nuna baki isaba, ƙaunar kice tamin yawa a cikin zuciya ta. Wani iri mummy taji a damtsen ta, wani yamm gurin yakeyi mata, ƙoƙarin kwace hannun ta tayi ya kuma riƙe wa da karfi, "pls ka barni mana" "Promise me bazaki tafi ba koda na sake ki" "Eh bazan tafi ba, sakeni" Sakin ta yayi yana daɗe babbake hanya wai duk don karta wuce "pls mehtab uzurin ya isa haka, hakurina ya ƙare akanki, kullum kice saboda Madam ɗina ne bazaki Aureni ba, to yanzu ma babu ita amma kin ƙi yarda dani a matsayin miji, anya kuwa zaki taɓa kauna ta?? "Wai ni nace bana kaunar ka ne?" Maganar ta kufce ta fito daga bakin mummy ba tare data shirya ba, saurin cewa tayi "Ni Kawai dai Auren ne banaso" don ta gyara zancen ta. Ganin har ya samu tana yi mishi magana yasa yace "go inside we will talk later, but pls kisa lafayar ki akwai mutane sosai a gidan" Kunya ce Sosai ta kama mummy domin ita sam tama manta haka take ziƙau daga ita sai doguwar rigarta, cikin sauri ta warware lafayar ta fara naɗa wa da sauri sauri..... Aseey da Aayann me zasuyi idan ba dariya ba, Sosai Abin ya basu dariya, saving ɗin video ɗin da yai musu Aayaan yayi sannan ya saka wayarshi a aljihu...... Nawaz kuwa tana chan sai shiga take tana fita domin yau ta samu sake, ado tasha da wata ocean green ɗin abaya mai design a kirji da baya, ta wadatu da swarovski stones sai walwali yakeyi. Duk wannan Abin da akeyi ita bata sani ba, tadai san Aayaan ya haɗa walimar duka dangi.... Tun kafin karfe ɗaya zancen Auren mummy da Colonel ya cika gidan, me Naufal da fudail zasuyi inba murna ba, sai nemanta sukeyi lungu da saƙo amma babu ita ba alamar ta. Nawaz kuma sai taji gaba ɗaya kunya ta kamata, to yanzu Shikenan colonel ya zama daddyn su na gaske? Itama mummy nada miji yanzu kenan.... Ɗaki Takoma ta cire rigar jikinta ta chanza da wata cotton mara nauyi, so takeyi ta samu ta kwanta amma su hassu sunki barinta, yanzuma tana kwanciya sai gasu, shiru tayi tana tunanin ko zata gudu ɗakin Aayaan ne kawai kila idan achan ne zata samu ta huta. Ta ɓangaren mummy kuwa suna chan ƙuryar ɗaki itada ummin Nawaz da mummyn sarfraz, faɗa sukeyi mata akan tace musu "itafa bata son auren" "Lallai ne! Ai kuwa tun wuri ki gyara, irin wannan Babban mutum haka yace yana sonka ai abin arziƙi ne babba, kuma in banda abinki a ina yin aure ya taɓa zama laifi?kuma ki kalla kaf cikinmu waye beda Aure? Kece Kawai to ke ko irin sha'awar nan ma bama baki kullum muna samun lada ke kuma kina zaune fanko? To nidai Ina baki shawara ne a matsayin ƴar uwa, gara ki rungumi mijinki ku zauna lafiya tunda dai an rigada an daura auren" jawaban da mummyn sarfraz tayiwa Mummy kenan Ita kuma ummin Nawaz cewa tayi "Nasan hakan yana da zafi, zakiga kamar ya nuna miki karfin iko ne, amma ba haka bane tsabar soyayyar dayake yi miki ce tasa yakejin tsoron kada ya rasaki gaba ɗaya, yanzu dai haƙuri zakiyi ki rungumi mijinki kamar yadda mumyn sarfraz tace, kuma ai mace kwanciyar hankalinta gidan mijinta, domin duka duka kwana nawa da dawowar Abban Nawaz amma saina ke jina kamar an maidani sabuwa" Shiru Mummy tayi, tabbas gaskiya suke faɗa mata! Kota bangaren ta wani zubin idan taga mace tana yiwa mijinta hidima sai taji ta bata sha'awa, yanzu kenan idan tayi wani Abu na nuna ƙi ga auren zai zama kamar tayiwa Allah butulci kenan... "Nagode sosai sosai Allah ya saka da mafificin alkhairi, Allah ya bar ƙauna da zumunci, gaskiya inajin daɗin yadda kuke daukata a matsayin ƴar uwa, ada ina tunanin na rasa komai da kowa amma a yanzu da Allah ya haɗamu sai nake gamin na samu komai da kowa" amsar da Mummy ta basu kenan. Dariya sukayi Tare Da cewa "Amarya ta tashi ta shirya kada Ango da abokansa suzo bata shirya ba. Taro ya watse Lafiya inda Aayaan yasa aka maida kowa gida tare da sha tara na arziƙi, yanzu gida ya zama saura Mummy da Nawaz sai su Naufal saboda itama Aseey ta koma kamar yadda baban muhsin ya buƙata, Colonel shima ya gudu tun washe garin da aka Daura Aure, yayi hakan ne don ya bata iska har zuwa sanda zata sauka daga fushin da tayi, abinda be sani ba shine ummin Nawaz da mummyn Sarfraz basu tafi ba Saida suka tabbatar sun cusa mata son Auren a cikin zuciyarta. Kwance Aayaan yake yayi flat a Saman gado inda Nawaz ke kwance saman ƙirjin shi sai faman shagwaɓa take tsula mishi "Nifa sweetheart mara ta ciwo takeyi, ji nake wani abu ya cure min a guri daya duk ya dameni." "Sweetheart kece fa kika riƙa yawo saboda kinga bana kusa dake, hannu yasa a daidai marar ta don ya duba, mamaki ne ya kamashi jin tudu sosai a gurin gashi yayi ƙarfi , tsabar firgici besan sanda ya tallafota ya tashi zaune ba, sauke ta yayi a jikinshi ya kwantar da ita yana duba cikin. A fili babu komai amma idan ya taɓa sai yaji yayi mishi tauri, "dear ko asibiti zamuje?" "No! Bazanje ko ina ba bayan kwanaki haka ka ɓata kusan awa biyu kana Abu ɗaya amma ya nuna babu komai, ashe kuma akwai, yanzu tunda ba komai nake jiba kuma yana motsi kawai mu barwa Allah komai" "But dear...... Bata bari ya ƙarasa fadar abinda yayi niyya ba tace "Allah nace fa" "Okay to! Allah ya tabbatar mana da Alkhairi" "Ameen" Nawaz tace tana ƙoƙarin tashi, "dear please a barni in gaisa da little Aayaan" Chuno baki tayi Alamun itafa babu dama "Ni dai gaskiya yaya yanzu zaka hana mutum sakat, kuma ko nace ka dena ba denawa kake yiba don zama kake kamar kurma." "Haba sweetie na! Kinga fa rabon da mu gaisa tun sanda mukaje gidan Daddy colonel fa, kuma kinga lokacinma bamusan yana nan ba sai daga baya" "Ni dai yaya gaskiya so kake kawai ka tayar min da hankali ina zaman zamana" "Dear pls mana! Bakiga ƙoƙarin dana yiba ne? Ko so kike inada mata na riƙa ciwon mara kamar gwauro" Shiru tayi, tasan Aayaan yana matuƙar ƙoƙari akanta, daga yanayinshi kawai tasan me yawan bukata ne, amma duk don kada ya sata a damuwa yake kyaleta, itama fa yau ya kamata tayi wani abu da zaisa shi yaji eh itama fa tana sonshi. Samun kanta tayi da haɗe bakinsu guri ɗaya, French kiss ta bashi sosai, shuko Aayaan gaba ɗaya mamaki ya kamashi na ganin abinda Nawaz tayi, be gama wannan mamakin ba yaji tasa hannu tana cire mishi boturan riga, tana gama wa tasa hannu ta zage zip ɗin wandon shi. Shi dai Aayaan a wannan rana dai kasheshi ne kawai mamaki beyi ba, amma ya firgita da lamarin Nawaz domin ita taja ragamar komai, sosai ya samu gamsuwa fiye da ko yaushe. Sai bayan komai ya lafa kuma kunya ta rufe Nawaz, kasa motsawa daga inda take tayi, lura da hakan da Aayaan yayi sai yaketa tsokanar ta yana cewa shifa tayi matuƙar burgeshi sosai, kuma ta sashi farin ciki matuƙa, idan da hali ma shi yana buƙatar ƙari. Dai dai kunnen ta yasa bakinshi inda yace mata "dear nifa wata sugar naji kin ƙara ne! Pls meye sirrin?" Tsabar kunyar data kama Nawaz bata san sanda tayi ƙundumbala daga kan gadon ba tayi cikin bathroom da gudu, tashi yayi shima ya rufa mata baya yana dariya °°°°°° *Aseey* Ko bayan ta koma england rasa sukuni tayi, tanaso Daddy colonel yasan cewa har yanzu shi mutum ne duba da dadewar da marigayiya tayi tana ciwo, kuma bata tunanin Mummy zata saki jiki dashi sosai har ta faranta mishi. Samun kanta tayi da tuna Aunty khatoume, babu jinkiri kuwa ta kirata ta faɗa mata cewa mummyn su tayi aure sai dai ga yanda Auren ya kasance, duk Abinda Ya faru ta bata labari sannan daga bisani tace tanaso ta kira mummyn ta bata shawarwari sannan ta tura mata da magungunan gyaran jiki na musamman kuma emergency, sai dai ta roƙe ta akan cewa don Allah kada ta faɗa wa Mummyn cewa ita ta faɗa mata, tace Kawai ji tayi itama. Sosai Aunty khatoume taji daɗi jin cewa Mummy tayi Aure, domin dama tun tuni take fama da ita akan tayi aure Amma taƙiyi, Hakan yasa taci alwashin tura mata magunguna na musamman domin ta rikita colonel. °°°° A chan Zaria kuwa ko bayan sun koma Abban Nawaz baya wani kula umma, sam ya fita sabgar su ita da Jamila, ita ko umman bata damuba sam illah istigfarin ta data dage dayi, tuba kuwa harta gaji dayi. Basu samu sauƙin abun Abban Nawaz ba har saida ummin Nawaz ta sameshi tace mishi jamila fa fyaɗe aka yi mata a makaranta kuma da dare ne shiyasa koda akabi kadu ba'a gane waye ba, ta ƙara dace mishi sun bar maganar ne saboda kada sunan jamilan ya ɓaci. A Ranar kuwa Abban Nawaz ya shiga ɗakin umma, har zama yayi a gefe tare da tambayarta ya jiki. Tun daga ranar suka samu sauƙin abubuwa da dama, jamila kuwa ta warware sosai domin duka aikin gidan ita takeyi dukda cewa ummin Nawaz na hanata yin wasu abubuwan. Ranar da Umma taji ƙaryar da ummin Nawaz tayiwa Abban Nawaz akan cikin Jamila Saida tayi kuka, wato ita ada kullum neman hanyar da zata tozarta ta take amma yanzu itace ke nemar musu sasanci a gurin kowa. °°°°°°°°°° *Bayan wasu watanni* Abubuwa da dama sun faru, ciki harda tarewar Mummy da Colonel, sosai colonel ya samu kanshi cikin wata sabuwar duniya, hakan yasa ya dage wajen kula da Mummy yana ririta ta sosai, kullum yana nakiƙe da ita kamar ya cinye ta, datayi motsi kuwa zaiyi saurin tambayarta meya faru, itama Mummy ganin yadda colonel ɗin ke kula da ita, ga kuma su Naufal suma kullum cikin yi mata hidima suke yasa itama ta kwantar da hankalinta ta saki jikinta suke farantawa juna. Yauma kamar kullum suna zaune a dining suna yin lunch, Naufal na gefen Mummy yana cewa ta bari yabata a baki tunda Daddy yau be fito da wuri ba. Fudail sai dariya yakeyi yana kallon su, Domin Mummy taki yarda shi kuma sai ƙoƙarin saka mata cokalin a baki yakeyi, ana haka colonel ya fito yana duba agogon hannun shi "kuyi sauri kuzo muje kada muyi lattin ɗauko su kun....... Kafin ya ƙarasa Magana sukaji ana knocking ɗin kofa, Daddy colonel ne ya ƙarasa bakin Kofar ya buɗe.... Sakin baki yayi yana kallon su, Aayaan ya gani riƙe da Nawaz wadda daƙyar take tafiya saboda tirtsetsen cikinta. "Son yanzu fa nakeso muzo mu ɗauko ku, how manage kuka rigamu isowa?" Murmushi Aayaan yayi yana cewa "ashe flight ɗin 7:30am ne nace maka 8:00am" Okay to sannun ku da zuwa, mummy ce tayi saurin ƙarasawa ta riƙe Nawaz Daddy kuma sai Sannu yake jera mata, Naufal ma kamar ya fashe da kuka sanda yaga Nawaz ɗin. "Anya yaya Captain ba ƴan-biyu bane a cikin Aunty kuwa?" Fudail yace cikin jin tausayin halin da yaga Nawaz ɗin a ciki. Lallabawa Mummy tayi ta zaunar da Nawaz ɗin a saman kujera sannan ta waigo gurin Aayaan wanda idonsa yana kan Nawaz ɗin. "Sannu da ƙoƙari Aayaan! Yanzu dama haka daughter take fama Amma shine kaki Kawo mini ita Saida nayita fama da kai? To yanzu yaushe ne EDD ɗin ta?" "Kiyi haƙuri mum! Nifa naso ne ace sai dai ku gammu da jinjiri, ko yanzu ma Kawai don kin matsa ne" Sakin baki mummy tayi tana kallonshi, su kuma su Daddy me zasuyi idan ba dariya ba. "Ƙaniyarka Aayaan! Cemaka nayi yaushe ne EDD ɗinta? Ba surkulle nace kayi min ba" "Ai EDD ɗinta ya wuce tun shekaran jiya ne!" " Wai me ke damun kane Aayaan...... Bata ƙarasa zancenba tayi kan Nawaz da sauri tana rike ta ganin yadda ta fara murkususu alamun naƙuda....... *Pls kuyi haƙuri, naso ace wannan ne last page Amma naga yaƙi ƙarewa, don haka in'sha Allah sai zuwa gobe zamu yi last page ɗin* Matar Rasheed ❤️*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀* *92* *LAST PAGE* 😭😭😭 *Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji* Shima Aayaan a rikice ya ƙarasa gurin Nawaz ɗin yana cewa "me ya faru?" "Naƙuda ce! kama ta mu tafi asibiti" cewar mummy tana riƙe hannun Nawaz cikin nata, Alamun bata kwarin gwuiwa. "Hankalin Daddy Sosai ya tashi shima ganin cikin ƙankanin lokaci Nawaz ta fita daga hayyacinta, tunawa yayi da maman su Naufal, duk sai yaji zuciyar shi babu daɗi, suma twins wato Naufal da fudail sai sukayi ɗaki suna sharar ƙwalla. Shikanshi goga Aayaan ɗin sai ya rasa duk wani kwarin gwuiwar shi, gani yake kamar mutuwa zatayi, "Son be strong! Ɗauketa muje mota, kaida ita sai ku zauna a baya Ni sai nayi driving ɗin." Ciccibarta yayi zuwa motar ita kuma Mummy ta shiga ɗaki Don kwaso siyayyar da tayi ta haihuwar duk da bata san me Nawaz ɗin zata haifa ba. Driving yakeyi yana addu'ar Allah ya sauketa lafiya, domin ya gama lura da Yadda Aayaan ya sallamawa Nawaz ɗin duka rayuwarshi, yasan idan ta mutu to Aayaan ɗin shima sai dai ya zama kawar gwawa ce ke rayuwa cikin Duniya. Mummy ma sai addu'a takeyi, bini bini take waigowa tana duba Nawaz ɗin, shikuwa me gayya Aayaan duk yabi ya rungumeta sai sannu yake jera mata. Nawaz dama tun suna jirgi take fama, daure wa kawai takeyi, saida suka isa gidan ne abin yaci ƙarfinta, addu'oi takeyi a cikin ranta iri iri, idan ta kama wannan saita saki wannan. Ɗan sauki taji sanda ta fara karanta *"Allahummah la sahla illah ma ja'altahu sahla, wa'anta taj'alal huzna iza shi'ita sahla, Allahu, Allahu, rabbi, la ushrika bihi shai'a"* sosai take ta maimaita ta a cikin zuciyarta ta har Saida ta fito fili, duk ta jiƙe da zufa tsabar azaba, Ayanda take ji daba don Mummy da Daddy suna kusa ba tanaga kila saita zabgawa Aayaan mari, ya wani kanainayeta bayan ita kadai tasan irin azabar da takesha. Da gudu nurses suka fito da gadon da za'a ɗora Nawaz akai domin takai gejin da bazata iya takawa da kafar taɓa. ɗora ta Aayaan yayi yana binsu cikin hanzari, mummy kuwa tsabar damuwa rungume colonel tayi ta saka kanta a cikin ƙirjinshi ko zata samu sauƙi. Sanda za'a shiga labour room dinne wata daga cikin nurses ɗin tace wa Aayaan "yallabai iya nan zaka tsaya domin maza basa shiga" Kofar da take ƙoƙarin rufewa yasa hannu ya riƙe tare da cewa "Matsa ki bani guri Kafin nayi ball dake! Halan kece kika yi mata Cikin!" Yadda taga idon Aayaan ɗin yayi jajir ga jijiyoyin kanshi duka sunyi ruɗu-ruɗu yasa ta kauce ta bashi guri, fita tayi don taje ta faɗawa Babban doctor. Shi ko Aayaan be jira komai ba ya gyara mata kwanciya a saman gadon tare da janyo table ɗin da ake ɗora duka abubuwan buƙata, Ruwan naƙuda yasa mata sannan ya ɗura allurar oxytocin a ciki. Sauran nurses ɗin tsaye sukayi suna mamakin wannan lamari. Damƙe hannuwanshi Nawaz tayi tana cewa "yaya pls idan na mutu ka yafe min" Ƙara rike hannunta Aayaan yayi tare da cewa "pls kidena cewa haka, lafiya kalau zaki haihu in'sha Allah" "Yaya azabar tayi yawa, bansan yadda Zan kwatanta maka yadda nakeji ba" "I'm sorry, pls be strong! I need you, mum need you, dad need you, ummi need you, Abba need you, Aseey need You, and last of all babyn da zaki haifa shima yana buƙatar ki fiye da kowa, pls ki taimaka mana" Dai dai nan Dr Uthman ya shigo ɗakin don ganin waye wannan me ƙarfin halin, shiru yayi yana kallon Aayaan Sannan yace "buddy ashe kaine, yanzu wata nurse ta kawo min ƙara wai wani ya shiga ɗakin amsar haihuwa kuma wai har yana ce mata zaiyi kwallo da ita" "Dr nine, saukar mu kenan daga England madam ta fara naƙuda, shine mukayo Nan, ita kuma ta tsaya tana min zance" "Ayyah! Allah ya raba lafiya, ka duba komai babu wata matsala Koh?" "Eh babu, riga kawai za'a bani na chanza mata, sannan duka nurses ɗin nan zasu iya tafiya, idan ina buƙatar wani abu zan danna mic" "Okay to babu komai, ke mariya ɗauko mishi rigar naƙuda, ku kuma ku biyoni " Abinda Dr Uthman yace kenan tare da fita daga ɗakin Itama mariya tana bashi rigar ta fita daga ɗakin. Doguwar rigar jikinta ya zame mata cike da kulawa sannan yasa mata rigar. Ko minti ɗaya beyi da gama sa mata rigar ba ruwan faya ya fashe, matso da plate ɗin almakashi yayi Sannan yasa hand gloves, bazai iya kallon jikanta ba sai kawai yace ta riƙe duka hannuwanshi tayi pushing. A haka dai sukaita gwagwagwa har Allah yasa tayi wani yunƙuri me ƙarfi saiga baby ta fito, rasa me Aayaan zaiyi yayi don farin ciki, hannu yasa ya ɗauki baby ɗin tare da daidaita cibin yana yanke wa, gefen hannun daman Nawaz ya ajiye ta tare da yiwa Allah tasbihi a cikin zuciyarshi yana ayyana ya mummy zataji idan tasan mace Nawaz ta haifa? "Ga Mumtaz (Biyunin mummy,wato maman Sarfraz) kiyi mata addua, Domin ke kadai kikasan irin azabar da kika sha." "Nagode, Nagode, Nagode sosai sweetheart, bansan dame zan iya biyan kiba san...... "Yaya cikina" Abinda Nawaz ta iya cewa kenan cikin murya mai nuna zallar jigatuwar da mai ita yayi. Da sauri yasa hannun shi a Kasan rigar donjin ko mahaifa ce ta tawo, ga mamakinshi sai yaji kan wani jinjirin ne ke ƙoƙarin fitowa, jikinshi har rawa yakeyi tsabar farinciki, taimaka mata ya riƙa yi tana pushing a hankali, cikin ikon Allah kuwa taji wani karfi yazo mata ta turo shi duka zuwa mararta, ai kuwa sai wani uban ihun jinjira ya cika ɗakin, tare suka fito ita da mahaifar lokaci ɗaya, bata jira komai ba tun kafin Aayaan yakai ga yanke mata cibi ta turmuka hannunta a baki ta fara tsotsa. Duk Aayaan ya rasa yadda zai yi, farincikin yayi mishi yawa shi kaɗai, yanaso ya samu wanda zai taya shi. Mumtaz tana gefen Nawaz ɗin inda ya ajiye ta tun dazu, dama ita tunda aka haife ta batayi kuka ba, ta biyun ce akoke kuma acici, gaba ɗaya ta tsotse ruwan haihuwar Sannan taci gaba da yanyara ihu. Zanin gadon dake saman ɗaya gadon ya janyo ya saka su duka a ciki ya nannaɗe Sannan ya maida su saman ɗaya gadon. Yanzu gaba ɗaya ta Nawaz yakeyi, she look so pale, gaba ɗaya idonta ya rufta fuskarta tayi pink bakinta kuwa yayi jajir dashi. Dagota yayi ya tallabe kanta yana sakin mata murmushi "dear har two kid's? I Don't know what to do, me zanyi miki ne?" "Son da kakeyi min nakeso Kaci gaba dayimin har zuwa ƙarshen rayuwata" Abinda Nawaz tace kenan cikin dasashshiyar murya "Har dai wannan ne to kisa a ranki ƙaunar da nakeyi miki zanma ƙara ninninkata ne har zuwa sau babu adadi, Nagode sosai dear" Maida ta yayi ya kwantar tare dace mata "bari na nemo Doctor mace ta gyara miki jiki, bazan iya kallon yadda honey pot ɗina yasha wahala ba, i love You" Fita yayi yana waiyayensu kamar zai cinye su duka, a bakin ƙofa yaga Mummy da Daddy sai zarya sukeyi suna tsumayen jin ance ta sauka, mummy ce tayo gunshi da sauri "Son ta sauka kuwa?" Ƙarasa cire hand gloves ɗin hannunshi yayi yana cewa "mum and dad ta haifi twins, all girls" Rukunkume dady mum tayi tana jin kamar tashiga ɗakin ta kwaso yaran, amma babu hali. Office ɗin Dr Uthman ya ƙarasa inda yace pls a bashi mace doctor wadda ta haura shekara arba'in yanaso zata gyara Nawaz ɗin, wai beson yara saboda sun cika rashin kunya, tare da ita suka tawo, a bakin kofar ya amshi kayan jinjirayen dake hannun mummy Sannan suka shiga ciki shida doctor munira, Allah Sarki Nawaz har barci ya ɗauketa. Cikin ƙankanin lokaci aka shirya twins tsaff dasu, itama Nawaz lokacin ta tashi, kwashe mata jinin doctor tayi sannan tayi mata allurorin da zata ɗan ji kwarin jikinta, shiko Aayaan yana zaune ya riƙe hannuwanta sai godiya yake yi mata, saida aka gama shirya su tsaff Sannan Doctor munira tace taza tafi, hannu Aayaan yasa a aljihu ya ciro kudi masu kauri ya miƙa mata tare dayi mata godiya "Pls idan kika fita kice su mummy su shigo" Abin mamaki su Naufal ne suka fara shigowa, fudail ne yayi sauri ya sunkuci akoke, shikuma Naufal ya ɗauki Mumtaz tare da cewa "ai sai kayi! duka dai mata ne balle kace" Duk halin da Nawaz take ciki saida murmushi ya kufce mata, wato dai su ƴan biyu sai dai a barsu, ko sun girma sai sunyi wannan fadan nasu na gado. Mum da dad ne suka biyo baya, "Au daga Zuwan yara duniya zaku fara wajiga su ko? To duka ku ajiyesu" cewar dad yana nufar inda Nawaz take " Sannu daughter na, yanzu za'a kawo miki farfesun kajin danasa ayi Miki, fatan zakici?" Rufe ido Nawaz tayi don kunya, ita kuma mummy ajiye flask ɗin Ruwan zafin dasu Naufal suka tawo dasu tayi tare da basket ɗin da suka zubo kayan tea, a gurguje ta haɗa wa Nawaz ɗin tea me kauri Sannan ta mika wa Aayaan tace ya bata tasha, A Hakan ma su Naufal sai musu sukeyi wai kowa sai dai yace tashi tafi kyau, mummy ko tanaso ta gansu amma kunya ta hanata amsa, Daddy ne ya lura da hakan "kai ku kawo yaran nan muma mu gansu, Amsar ta hannun Naufal mummy tayi shima Daddy ya amshi ta hannu Fudail. Sanda Mummy tayi arba da fuskar yaran saida gabanta ya fadi, Domin sak kama sukayi mata da Aayaan sanda yana jinjiri sai dai waɗan nan sunfi Aayaan fari duba da farin Nawaz suka kwaso. Shi dai Aayaan tunda ya lura yaran kalau suke saiya Maida hankalinshi duka akan Nawaz.... Basu suka koma gida ba sai bayan magrib, achan gidan har wasu sunzo waɗan da basuda nisa musamman Yan uwan dad da suke Abuja. Basu daɗe da komawa ba saiga tawagar mummyn Sarfraz da Sarfraz ɗin harda Hajiya hassu😉 dasu bandi, da mamanta., Aseey kuwa ta kira yafi sau Goma,ji take kamar tayi tsuntsuwa ta iso acikin daren. Cikin yan kwanaki gaba ɗaya gidan ya cika da mutane ta ɓangare daban daban, yara kuwa daga nan sai chan danma su Naufal sun kasa sun tsare akan kada a wahalar musu da mata, shima Aayaan Saida Mummy ta wanke shi fess sannan ya samawa Nawaz lafiya, amma da yana nakiƙe da ita duk Yan Barka ma anan suke tarar da shi. Sosai mummyn Sarfraz take kula da Nawaz, abinci take tasa mata agaba saita cinye, sannan ga tea, ga farfesun naman rago da Daddy colonel yasa akeyi mata kullum, suma su Naufal kullum da babbar ledarsu ta Kayan marmari idan suka fita yawo tare dasu Sarfraz da bandi,wai duk na toshiyar baki. Ana gobe suna kuwa gidan babu masaka tsinke, kowa ya hallara harda su inna talatu dasu jamila da Fauziyya, sosai suka Yadda da kalmar *hassada gamai rabo taki ce* ganin Irin gidan da Nawaz ɗin take Aure, sanda kuwa sukaga yadda Aayaan yake nan nan da Nawaz Saida sukaji kamar ƙasa ta tsage su shige. Akwati biyar Mummy tayiwa Nawaz da yaran na fitar suna, ita kuma Aseey uku sai Daddy colonel shima biyar, kuma shi ya ɗauki nauyin yanka, kowa rago da tunkiya ga kuma manyan shanu guda biyu. Mai gayyah kuwa wato Aayaan, Aishi akwatin ishirin yayi, Nawaz goma yaran kowa biyar biyar, sannan ya gwangwaje su duka da sarkokin zinare da abun hannu da zobuna. Kowa sai baza ido yake yana kallon arziƙi a inda yake. Ranar suna kuwa Nawaz haka ta zama kamar wata tauraruwa, duk inda tayi ido na Binta, wasu najin daɗi wasu na cewa dama sune wasu kuwa haushi sukeji don babu halin nunawa ne. Sai shiga take tana fita cikin manya manyan leshina saƙar ƙasar swiss da Australia waɗanda daka kallesu zasu bayyanar maka da kudinsu a fili, taro yayi taro babu wanda be halarta ba sai wadanda ba'a rasa ba, kamar ummin Nawaz, ita dinma anyi anyi tazo tace bazata iyaba ita kunya takeji, wai bayan suna zata je taga kishiyoyinta, sai umma wadda jikinta ne yasa batajeba itama. An raba kyaututtuka kamar ba'a san zafin kuɗi ba, inda wasu daga ciki sarfraz ne ya ɗauki nauyinsu jin ansa sunan mahaifiyarsa, sai Mummyn Sarfraz da Aseey. Mutane kowa sai san barka, kowa da Atampopinshi da jakunkuna da bokitai iri iri, Mumtaz da Rahma (anyiwa Nawaz kara akasa sunan mamanta) sunyi goshi sosai inda ake ta turo musu da kyautar kuɗaɗe da kayayyaki har daga wajen Nigeria. Taro ya watse Lafiya inda washe gari kowa yayi haramar komawa gida, a hankali gidan ya dawo dai dai sai na jiki sosai suka rage, irinsu Aseey dasu Sarfraz da Mummyn Sarfraz, su Jamila da Fauziyya ma suna nan Saboda mummy tace su tsaya sai su koma tare dasu Sarfraz. Kuka Sosai Nawaz ta riƙa yi sanda Aayaan ya bata takardun kamfanin abaya ɗin shi dake Dubai yace ya mallaka mata halak malak tukuicin twins data bashi, suma duka saida ya Mallaka musu nasu ɗai ɗai. "Wannan wane Irin abu ne yaya, Company pa kacokan fa!" "Hhhhhh sweetheart nifa dariya kike bani, wai kin manta abubuwan dake kika mallaka min ne? Ko akwai injin dake haɗa yara ne? Kuma akwai inda kike tunanin zan samu natsuwa ne bayan gurinki, nifa ke nake kauna kuma ke nake so, ke nake sha'awa kuma ke kike birgeni, bani da wani burin daya wuce na ganki cikin farin ciki da walwala...." Rungumeshi tayi tanata jero mishi addu'oi da godiya. Haka Nawaz taci gaba da jegon ta cike da kulawa tako wane ɓangare, abinci me cike da lafiya da gina jiki ake bata, shiyasa tayi fess abinta yan biyu ma sam babu me cewa guda biyu ne domin sunyi kuɓul kuɓul abinsu. Gaba daya babu abinda takeyi saboda Daddy colonel ya ɗauko kanwarshi ita keyi wa Nawaz ɗin wanka da yaran, kuma da'an shiryasu su Naufal zasu ɗaukesu sai dai in anzo basu nono. Bayan suna da kwana biyar Mummy ta turawa Aunty khatoume kuɗi tace ta tawo tazo tayiwa Nawaz gyara har tayi arba'in. Nawaz mamakin irin kaunar da mummy takeyi mata take, Saboda wasu iyayen mijin sam babu ruwansu da matar ɗa, kuma ko labari sukaji kan cewa tana shan magungunan gyaran jiki faɗa akeyi dasu, saboda cewa sukeyi zata mallake musu ɗa, Amma ita Mummy da kanta take sawa ayi mata. Bayan zuwan Aunty khatoume da kwana uku ne aka nemi su Aayaan tare da colonel. Ansha fama Kafin ya tafi, mummy ma daɗin tafiyarsu taji saboda tasan Aayaan hanasu sakat zaiyi, kuma itama zata dan samu damar da zata ƙara gyara kanta wa Colonel, domin bajintar da yayi a sunan Nawaz ko ɗan daya haifa a cikinshi yayiwa haka sai an yaba mishi balle kuma. Shima colonel saida mummy tayita fama Sannan suka tafi. Koda suka tafi basu saniba ashe an haɗa musu walimar ƙarin girma ne, inda shima Aayaan an cire sunanshi daga cikin masu zuwa yaki sai dai yanzu ya riƙa yin training ɗin wasu. Saida sukayi sati Uku tukuna suka dawo, shima da kyar domin Dukansu ji sukeyi kamar suyi tsuntsuwa su tawo gurin matansu. Ranar da suka dawo saura kwana uku Nawaz tayi arba'in, gaba ɗaya Aayaan rudewa yayi da yaga yanda Nawaz ta koma, ga ƴan biyu sunyi manya-manyan abinsu kamar sunyi wata uku, kana musu wasa zasu hau yi maka dariya. Yadda Aayaan ke rawar ƙafa a kan Nawaz yasa Mummy tasa aka kulleta tasan sarai saiya maida musu da aiki baya kuma saura kwana uku a gama. Aayaan kuwa kamar yayi hauka haka ya koma, babu yadda beyiba akan Mummy tayi hakuri amma sam taki kallonshi. Kuma a ranar data cika arba'in ɗin suka daga zuwa maiduguri Saboda Nawaz ɗin tayi yawon arba'in, saida Nawaz ɗin tayi sati tana yawo gidajen ƴan uwa kama daga dangin daddyn Aayaan danata kakannin, haƙurin Aayaan karewa yayi yai tafiyar shi basusanma inda yake ba. Daga nan ne kuma suka koma Zaria, Ummin Nawaz taji daɗi Sosai ganin yarta ta koma Babbar mace Sosai, kuma kowa ya kalleta yasan tana cikin kwanciyar hankali. Shima Abban ta haka yaketa nan nan da ita, kuma ƴan biyu kullum suna gurinshi. Kwananta biyu a gida saiga Aayaan yazo, domin yayi yayi amma ya kasa daurewa daga nisantarta da yayi. Ganin hakan nema yasa Abban Nawaz ɗin yace su shirya su koma, saida suka biya gidan mummyn Sarfraz itama sukayi mata kwana ɗaya, hassu da Sarfraz sai santin Yan biyu sukeyi, barinma Sarfraz yaji labari. Suna dira a Abuja Aayaan yace shifa Allah ya kasheshi sai an bashi matarshi sun koma england domin yama rigada ya sayi ticket kuma gobe da safe jirgin zai tashi. Mummy ce tace bazata koma ba sai Yan biyu sunyi Kwari, misali koda wata huɗu ne suyi. Ganin abinfa na Mummy da gaske take yasa Colonel yace wa Aayaan ya ɗauki matarshi su koma, domin yasan Aayaan ɗin yayi ƙoƙari. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° *ENGLAND.......* Koda suka sauka a England ɗin sai Aayaan yayi banza da ita, wai shi ala dole fushi yakeyi da ita, ita kuma Nawaz da taga haka sai itama ta shareshi domin yanzu tsoronshi takeji kada ta kuma samun wani cikin (niko matar Rasheed nace dama ya lafiyar kura balle tayi hauka?) Dafa yaga taƙi bi takanshi sai shi ya sauka, tana kitchen tana haɗa lunch saboda dama suna sauka a ƙasar ya samo musu wata baturiya me raino ya bata ɗaya sasan su, idan ba kuka suka yi ba bazata kawo suba. Kama kwankwasonta yayi ya ɗora kanshi a saman kafadar ta, "dear yanzu sam baki damu dani ba ko?" Kafin tace komai wannan mayen kamshin nata ya cika mishi hanci, take yaji abinda yakeji akanta ya ninku. "Bakai bane kahau yin fushi daniba kuma bayan Ni ban san me nayi maka ba" "Cikin muryarshi wadda ta fara chanza yanayi yace okay to na dena kuma kiyi haƙuri" "Okay Babu komai, ya wuce?" Kama hannunta yayi"zo muje kiga wasu files" "Yaya ka bari na gama girkin kaji" Be jira komai ba yasa hannu ya kashe gas ɗin Sannan ya ciccibeta yayi waje. Koda suka je ɗakin babu wasu files daya nuna Mata illah susuce mata da yayi, cikin ɗan tsoro tsoro Nawaz tace "yaya pls fa! Kaga su mamaa two months suke fa?" Ganin bazata yarda ba yasa yayi mata kwance kwance ya kashe mata jiki yadda kome zaiyi bazata musa mishi ba, Aikuwa ranar idon Nawaz ya raina fata, domin ta gurzu a hannun Aayaan ba kaɗan ba, duka bashin wata biyun da beyi ba saida ya sauke mata su, koda tazo miƙewa kasawa tayi, sai ta koma ta zauna tare da fashe mishi da kuka, haka ranar tayita yi mishi raki shi kuma yana ta jinya.... Wata sabuwar shafin soyayya da kulawa Aayaan ya buɗewa Nawaz, har dai akace abu na Nawaz ne to baya wasa dashi sam. Itama bayan su maman Sudeis da fatima an kawo sababbin zuwa Makarantar su, Wadda yanzu suna zuwan tane kawai don buɗe ido bawai don koyan wani abu ba, saboda suma sun rigada sun zama yan gari. Anan Nawaz taga yadda ake kula da lamuran miji, ake girmama duk wani abu daya shafi miji.... A groups groups na manyan mata suka sata a Whatsapp, hakan saiya daɗa wayar da Nawaz ɗin sosai, ita da bata damu da waya ba sai gashi yanzu tana dubawa sosai. Irin sabbin salon kular da Nawaz takeba Aayaan saiya sa ya ƙara sakar mata duka ragamar komai nashi..... Sanda Yan biyu sukayi wata shida ne suka koma Nigeria. Anan Aayaan ya biya wa Abban Nawaz da ummin ta Hajji da Umrah, umma kuma ya biya mata kuɗi aka fita da ita zuwa Egypt don ayiwa kafarta aiki tunda har zuwa Lokacin bata warke ba. Bayan sun tafi ne kuma yasa aka rushe gidan duka sannan aka chanza mishi fasali, Sosai ya kashewa gidan kuɗi don Kawai ya farantawa Nawaz rai. Kusan duka manyan ahalin Saida ya biya musu umrah daga ciki kuwa harda inna talatu, matasa kuma ya basu jari, waɗanda kuma suka gama makaranta ya samar musu akin yi. Anan ne wani daga cikin securities din Aayaan ya nuna yana son Jamila, Ba'a tsaya boye boye ba aka ce mishi bazawara ce harma ta haihu amma ɗan ya rasu, a haka yace yaji ya gani. Nanma dai duka Aayaan ne ya dauki nauyin komai aka yi bikin taro ya tashi Lafiya, itama Fauziyya ya bata jari me kauri. Umma kuma sanda aka dawo da ita, kafarta ta warke tsaf tana takawa saidai babu yatsu guda biyu. Haka ta riƙa kuka tana shiwa Nawaz Albarka, Ashe ita ɗin data tsana wata rana itace zata zame musu garkuwa, kuma bango majingina. Ita kanta Nawaz idan ta kalli kanta ta kuma tuna cewa itace ke koyarwa a HAYATUL ISLAM don a bata dubu Goma saboda su sai abinci, Lokacin da umma ta rufe store, sai taga kamar mafarki.... Komai yazo mata a bazata, itama bata tsaya iya nanba saida tabi duka kawayanta tayi musu sha tara na arziƙi. Kullum Cikin ƙara godewa Allah takeyi, ta kama mijinta da yaranta ta riƙe kam, haka ma Yan uwan ta dana mijinta, duk shekara idan akayi lissafin riba a Companyn ta da AAYAAN ya bata, bata cire komai a ciki, duka take rabawa yan uwa da abokan arziƙi. Haka idan suna england duk bayan sati biyu sai ta ziyarci su haidar da Aunty Aseey, sosai muhsien ya saba dasu mamaa, har cewa yakeyi shima mumynshi ta haifi irinsu. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Ita kadai ce take saukowa Daga cikin jirgin babu komai a hannun ta sai karamar 👛 purse, sanye take cikin farar abaya Wadda akayiwa kwalliya da Golden yellow, sosai rigar ta amsheta, domin ta haska ɗanyar farar fatarta. Idan ka kalleta zaka zata irin larabawan misra ɗin nan ce, kuma ba Lallai ka yarda tayi Aure Bama balle a kai ga haihuwa. Wai a hakan ma tana cikin tashin hankali ne. Cab ta tara ta kaita har Kofar gida, tana shiga ta rushe da kuka tun a bakin falour. Hankalin kowa tashi yayi ganinta ita kaɗai gashi kuma tana rusa kuka. Da sauri mummy ta tareta tana cewa "daughter ina Aayaan ɗin, ina su mamaa?" Suma dai su Colonel miƙewa sukayi saboda fargaba. Cikin muryar kuka Nawaz tace "duka suna england" "Meya faru kika tawo ke kaɗai?" Mummyn ta kuma cewa zuciyarta na bugun uku uku. "Mummy ashe tun wata huɗu da suka wuce yaya Aayaan ya lura inada ciki, saboda kada na gane sai ya siyo mini wani magani yace kullum nasha Guda daya, wai yana hana ɗaukar ciki kuma wai idan ina shan shi bazan kuma haihuwa ba sai bayan shekaru da yawa kum...... "Su Naufal dake gefe ne suka kwashe da dariya " "Au dama akwai sa'an ku Anan kenan, kun wuce ko kuma saina ci muku " Daddy colonel yace cikin faɗa, ai kuwa da gudu suka shige ɗaki suna dariyar dramar Nawaz da Aayaan Wadda bata ƙare wa. "Daughter go on muna jinki" mummy tace tana kallon Nawaz ɗin cikin fargaban me zata ce a gaba. To cikin kwanakin nan sai naketa fama da tashin zuciya da amai ga kwaɗayi, kuma inajin kamar ana motsi a ciki na, shine naje asibiti, da ya hana amma daga baya ya yarda naje." Ƙara fashewa tayi da kuka Sannan taci gaba "Shinefa a asibitin akace ciki gareni kuma har yafi wata huɗu, kuma da akayi scanning akace wai har yan biyu fa, kuma duka maza" Da gudu su Naufal dake labe suka fito suna murna, "wayyooooo daɗi, munata ƙara yawa" Duk yadda Mummy taso ta kanne Amma saida dariya ta kwace mata, shima Daddy Saida yayi murmushin manya ... "Lallai ne abinda son yayi kenan? To ai kuwa zamu haɗu, Naufal kira yayan ku kace daughter nanan kuma maza maza ya biyo flight ɗin yamma yazo ya sameni shida su mamaa" Zukar majina Nawaz tayi Sannan tace "mummy kumafa yanzu watansu mamaa takwas fa" "Kada ki damu ki barni dashi, ai zaizo ya sameni ne" Haka dai aka lallaba Nawaz aka samu ta hakura, koda Aseey taji labari kamar ta zuba Ruwa a kasa tasha don farin ciki, itama daman tanata fama da laulayin ƙaramin ciki. Kafin wani lokaci labari ya bazu a cikin dangi, inda itama hassu tana nan tana fama da nata ƙaramin Cikin, koda Sarfraz yaji labari sai cewa yayi Allah yasa itama hassu ta haifi ƴan biyu. Koda Aayaan ya iso cikin dare baice komai ba sai aikin lallashin Nawaz da yayi ta fama, haka dai aka haɗu aka bata baki ta haƙura akan zata bishi su koma sai dai fir mummy taƙi basu su mamaa, tace dama nata ne jira kawai take yi a yayesu, yanzu kuma tunda an yayesu ta dauki abin ta. Koda suka koma england ɗin sai Aayaan ya zama kamar wani sabon ango kullum yana nakiƙe da ita barin babu kowa daga ita sai shi....... *Tammat bi hamdulllah* *Komai farrare ne kuma kararre, amma banda ikon Allah* *Yau dai Allah cikin ikon sa yasa na gama wannan littafin na SARFRAZ lafiya, Alkhairin dake ciki Allah ya bamu ladansa, kurakuran dake ciki kuma Allah ya yafe mana.....* *Ina miƙa godiya ta ga duka members na* *MATAR RASHEED NOVELS* *AK SARAKI PALACE* *AK SARAKI NOVELIST GROUP* *INUWAR SHARRI FANS GROUP* *SANADIN HIJIRA FANS GROUP* *SIRRIN RUHI* *ASLI SMASHER FANS GROUP* *RUƊANI FANS GROUP* *FADAR AUTAR MANYA* *M&Z NOVELS* *WOMEN 24 TV NOVELS* *VIP 24 TV NOVELS* *HAUSA NOVELS 2K2* *ƘASAITACCIYAR MACE GROUP* *DAUDAR GORA FANS GROUP* *ROYAL STAR WRITERS* *Da dai sauransu, ina fatan zamu haɗu a littafina na gaba mai suna IZAYAR RAYUWA......* *08093215055 Number ta gamai buƙatar zumunci, gyara ko shawara, Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji tana ƙaunarku duka.* *29/5/2023 Monday* *9/11/1444 Monday* *Nagodeeee da ɓata lokacinku mai ɗunbin daraja da kukayi kuka bibiyeni har zuwa ƙarshen littafin.........* *Matar Rasheed ❤️*