Godiya ga dukkanin yabo sun tabbata ga ubangiji talikai mamallakin sammai da Kasai Allah . tsira da amincin Allah su Kara tabbata ga fiyayen halita annabi Muhammad (s. a. w) *godiya mara iyaka* GA dumbin mabiya litattafaina a Duk inda kuke cikin kasar Allah. ina matukar alfahari daku ina kaunarku kmr yadda kuke kaunata. “I will succeed. Not immediately. But definitely.” in shaa Allah. ✽‌»‌≿━༺🌹﷽🌹༻━≾»‌✽ Anas b. Malik (R.A) reported that Messenger of Allah ﷺ thus told him: *"When a non-believer does good he is made to taste Its reward in this world. And so far as the believer is concerned, Allah stores (the reward) of his virtues for the Hereafter & provides him sustenance in accordance with his obedience to Him."* حَدَّثَنَا عَاصِمُ بْنُ النَّضْرِ التَّيْمِيُّ، حَدَّثَنَا مُعْتَمِرٌ، قَالَ سَمِعْتُ أَبِي، حَدَّثَنَا قَتَادَةُ، عَنْ أَنَسِ بْنِ مَالِكٍ، أَنَّهُ حَدَّثَ عَنْ رَسُولِ اللَّهِ ﷺ *"إِنَّ الْكَافِرَ إِذَا عَمِلَ حَسَنَةً أُطْعِمَ بِهَا طُعْمَةً مِنَ الدُّنْيَا وَأَمَّا الْمُؤْمِنُ فَإِنَّ اللَّهَ يَدَّخِرُ لَهُ حَسَنَاتِهِ فِي الآخِرَةِ وَيُعْقِبُهُ رِزْقًا فِي الدُّنْيَا عَلَى طَاعَتِهِ* " . References: Sahih Muslim 2808 � ?cX僆茀$桝�欔凸W鸜竊甛厘预�,d衺n+NUm.}�櫏 葄忾g渽展家腅魖题�洄┉�9K 咕旱鹁粧穽墚Z� �驼xx�19L揣7s@熮e3i `{譜kル بِسْمِ اللَّهِ الَّذِي لَا يَضُرُّ مَعَ اسْمِهِ شَيْءٌ فِي الَْأرْضِ وَلَا فِي السَّمَاءِ وَهُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ [5/23, 21:56] Pretty Sk: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/share/p/14pZMxnDPB/ https://www.facebook.com/share/p/19hDk5NB65/ 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION💪✍️ (J.A.W) Rubuyu baiwa ce daga Allah, jajirtattu me kawai man iy amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi. ✏️ Typing free pages.................. 𝙍𝘼𝙎𝙃 Ɓ𝙊𝙔𝘼𝙔𝙔𝙀𝙉 𝙈𝘼𝙎𝙃𝙀Ƙ𝙄 Story & written BY SAKEENAT ABDULLAHI 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶✍️✍️✍️✍️✍ page 1 *********** ************* Kaduna south, Kinkinau, layin Massalacin Ustaz, unguwace ta masu wadata dai-dai misali. Tafe take cikin shiga na mutunci, hijab ne har ƙasa sai niƙaf, kwayan idanuwanta da ya sha uban kwalli kawai ake gani a jikinta, tana isowa jikin gidan nasu sai ga Mahafinta Malan Abdullahi Saleh Ustaz yafito daga cikin gidansu, cikin ladabi ta gaishe shi " Abba ina huni " " lafiya lau, har an dawo makarantan ?" " Eh Abba" " to Allah yataimaka " sannan ya shiga massalacin dan kiran sallan magrib. da sallama tashiga cikin madaidaicin gidan nasu wanda yahaɗu balaifi. ba kowa a tsakar gidan dan haka tashiga ɗakinsu. " Assalamu Alaikum " da kalman da tashiga ɗakin kenan, shuru ba'a amsa ba sai ta kunna globe din ɗakin take hasken lantarki ya haska ɗakin. babban ɗakine wanda yakeda gado irin na ƴan bodin guda 2 me hawa biyu, kenan guda 4, sai babban wradrobe guda biyu da madubi wanda ya sha uban kayan kwalliya. jakkanta tacire tare da cire niƙaf din tana kallon kanta a mirro, Alhamdullih ta furta tanamai kallon kyawun da Allah ya yi mata, bafara bace choculate ce sosai ga tsayin hanci da manyan idanuwa sai baƙaƙen gashin idon wanda za ka za ci tasa gashin ido ne. baza'a ce mata doguwa ba sannan baza'a kirata gajeraba daidai wadaidai tsayin nata. " Wai kinshigo dama ?" ta tsinkayi muryan yayarsu Hajara wacce ta ɗan miƙa daga kwancen datakeyi tana murza idanuwan ta. "Eh Aunty Hajara na dawo ashe kina sama kina barcin dai." "Uhmmmmm ni fa kar ku dameni" wata budurwa ta furta itama daga ɗayan bed din. "Lallaima Marry wai da ma baki daura girkin ba?" Hajara ta faɗa tana zaro idanuwa. take suka sauko suka fita da sauri harda haɗawa da gudu-gudu dan jin wasu masallanta sun fara kiran sallah kuma sunsan sallan magrib ne, sanyayyar murmushi tasaki tana mai cire hijab sannan tafita dan duba Umma kafin a shiga sallah. Babban ɗakin Umma tashiga da sallama, falon yasha kyau komai Ash and white ne, mai girma ne sosai, sannan ga kayan kallo a ɓari guda, bakowa a parlourn dan haka tanufi babban kitchen wanda ƙofansa ke ta ɓangaren yamma wanda takejin hayaniya sama-sama, su hudu ne aciki, Umma, Hajara, Maryam, sai Zainab da alaman ita ke girkin dan sai faman yanka albasa take yi. " ai barci yafi komai agunku, kuci gaba dayi ". Umma tafaɗa tana tashi daga kujeran da take kai. " ki ya ƙuri, wlh nama Maryam magana dan ita ce dayi shine tayi barci kuma ni bansan nima barcin ya ɗauke ni ba" " ki ya ƙuri Umma ban jin daɗi ne shine nakwanta bansan barcin ya ɗaukeni ba, kaina ke ciwo" Maryam ta faɗa da sauri dan jin Hajara zata ɗaura mata laifi " ya isa shi ke nan, kuje an shiga masjed" Umman tafaɗa a daƙile dan haka suke mayun barci danma zainab batada damuwa kusan koda yaushe tana Kitchen abinta " Umma barka da yamma " sai suka juyo suka kalleta dan basusan lokacin da tashigo ba " yauwa Ramlat ". Abinda Umman tafaɗa kenan ta huce ɗakinta, inda sabo tasaba, sam Umma bata wasa da ita irin nasauran yaran gidan. Hajara ce ta dafa mata kafaɗa tana cewa. " Sorry Ramlat " " ayya badamuwa, bara naje nai sallah." daga haka ta wuce fuuuu. " Wai yaushe Umma zata canza ne akan Ramlat? gaskiya banjina daɗin haka, ace ko magana mai tsawo bazatayi da ita ba" zainab ta faɗa tare da kashe gas dan ta kammala. " ha kane amma muci gaba da mata addu'a kawai danma Ramlat din ba ta da ruƙo a zuciya " cewan Hajara " Allah ya kyauta " abin da Maryam tafaɗa kenan. tare suka fita ta ƙofan cikin Parlour suka shiga babban ɗakinsu mai ƙofa biyu, kowannan su ya ɗauro alwala suka gabatar da sallah cikin jam'i kamar yadda suka saba, bayan sun idar, maraja'an karatun alqur'ani suka fara cikin daddaɗan muryoyinsu, musaffa sukeyi cikin futar da hukuncin kowani harafi na tajweed, su gunna, ƙalƙada dasu iddigami bigairi gunna da sauransu, ma sha Allah kowannansu gwanine cikin rero nashi shafin. binsu nai da kallo masha Allah, kowacce hijab ɗin jikinta ya haskata sosai, Hajara fara ce, ga dogon hanci da idanuwa daidai wadaida haka Maryam take itama dan akwai kama sosai a tsakaninsu, tsayi, launin fata da wasu abubuwa, Itako Zainab tafusu haske sai dai ita bawani tsayi garetaba tsayinsu ɗaya da Ramlat sai dai Ramlat dafisu body-shape mai kyau. kuma tafusu kyau dukda itace mai duhun cikin su, gashi muryanta yafi nasu ɗaɗi har suna so a zo ɓangaren ta dan ƙira'anta akwai daɗi da taushi, ana kiran isha suka kammala karatun tare suka gabatar da sallan isha. suna idarwa suka nufi babban parlour dan cin abinci. Umma suka samu tana cin abinci dan haka Hajara tazubo musu a babban flate suka hauci suna kallo a babban TV ɗakin, shirin Lavi da lena suke kallo a tashar Daɗin kowa TV. bayan sun kammala cin abincin suka cigaba da kallon TV sai can Umma tace " Kun san dai lokaci nata ƙaratowa dan gudanar da shagalin bikin ku, ke Ramlat har yanzu kinƙi fitowa da saurayi a haɗa da ke a huce gun ko? " " Umma ni banda saurayi ai ......." " uhmmm faɗa gas..." hararan da Umma ta yima Maryam ne yasa tayi shuru tana kallon ƙasa, " Nidai bawanan ba kije ki bincika, nasan bakya kula kowa amma ba zan yadda bakida samari ba, kodai zaki ba Abbuu zaɓi kawai daya aura miki wanda yadace, kin ga Zainab ma haka ne an ha ɗa ta da wani ɗalibin sa" " Umma wlh na amince koma wanene ni banda damuwa, kawai bana da ce ne duk wan'inda suka zo nema na sai na same su da wani ɗabi'a na daban" kanta a ƙasa tayi maganan cikin jin daɗin yadda yau wai itace da Umma ke maganan daya shafi rayuwarta. " shikenan zanma Abbuu magana kuje ku kwanta" daga haka suka shige ɗakin su rufewa sukayi suna dariya ƙasa-ƙasa. " Maryam kinga ai yafi a haɗa dukkan mu kawai a huta" " Haka ne Hajara zefi gaskiya" " Karfa ku manta ni shekara ta 18 ne, ku tweens (Hajara da Maryam) 22yrs kuke, Ita Zee 21yrs ......" " so what madam, oya get ready to marriage, wa ze ce ke ce ƙaramar mu bayan ki na da uban jiki " faɗin Zee tana kwanciya kan bed din ƙasan na Maryam. " Waima ina Sagir ? dayake nemanki a islamiya ne?" Maryam ta fa ɗa tana kallon Ramlat " wannan ai bazan iya auran shi ba, be da mutunci kar kiga yadda yake ma malaman makarantarmu, nikadai yake raga mawa saboda makarantar Abuu ne" " Allah ya kyauta " abinda Hajara ta faɗa kenan tana ka ra waya a kunne alaman amsa kira, Zainab kam barci ne ya dauke ta, Maryam kuma ana sana'ar ta chart da Usman, Hajara kuma waya take da wanda ze aure ta Muhammad. Ramlat kwanciya tayi ta na ta tinanin hirar ta da Umma, murmushi ta sa ki a hankali dan tinawa da rayuwar su ta da. End alƙalamin daga PRETTY SK.. [5/27, 18:34] Pretty Sk: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION💪✍️ (J.A.W) Rubuyu baiwa ce daga Allah, jajirtattu me kawai kan iya mfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi. ✏️ 𝙍̀𝘼̀𝙎̀𝙃̀ Ɓ̀𝙊̀𝙔̀𝘼̀𝙔̀𝙔̀𝙀̀𝙉̀ 𝙈̀𝘼̀𝙎̀𝙃̀𝙀̀Ƙ̀𝙄̀ ᑭᖇᗴTTY ՏK Page 2 TINANI Malan Abdullahi Saleh Ustaz mutun ne mahaddacin alqur'ani da hadisai yana zuwa guri-guri dan ba da fatawan addini, Malamin sunna ne sosai, yana da mata ɗaya Habiba wato Umma, suna rayuwa tare cike da tausayi da kulawa, shekarun su biyar da aure Umma tahaifa 'ya mace aka sanya mata Aisha, yarinya na kai 1yr ta koma ga Allah, sun ji ba daɗi amma su barma Allah komai dan yafisu son ta, a na nan wata rana a ka kawo wata yarinya dan ta musulnta a gun Abbuu, bayan ta amsa musulunci ta zaɓa suna Aisha, Abbuu yaji ɗaɗi dan yana son ya ga mace mai suna Aisha. labarin ta aka ba Abbuu ya tausaya mata, dan an kashe mata kowa a yaƙin boko haram, sai ya nemi daya riƙe ta a gunsa aikuwa aka bashi, bayan yazo gida ya bama Umma labarin ta, 'yar gudun hijira ce wace ta rasa kowa nata, Umma ta karɓe ta hannu bibbiyu. a haka su ka ci ga ba da rayuwa suna koya mata addini. Bayan wasu watanni Umma ta buƙaci Aisha ta zaɓa wanda take so a masu zuwa karatu gun Malan don ta aure shi, a nanne ta shaida ma Umma ita dai Abbuu kaɗai zata iya aura saboda ganin kyautatawan shi gare ta. Umma da ya ke maca ce mai sauƙin kai sai ba ta sa a ranta ba duk da ba taso jin haka ba, amma da Abbuu ya dawo ta shaida mai sai ya nuna indai ita ba ta da matsala shi ke nan. taso taƙi amincewa amma ganin Aisha duk tasauya ko abinci tadena ci, hakan yasa ta yadda aikuwa aka ɗaura auran, bayan ta tare su ka ci gaba da rayuwarsu cikin jin daɗi da kula da juna. a tare Allah ya basu ciki Umma ta riga haihuwa taƙara samun mace, Abbuu ya sa mata Aisha, ita ma Aisha data haihu mace yaƙara sa Aisha, dan shi be ƙi ko yara nawa ze haifa ya sa Aisha ba, yara sun fara girma har sun fara tafiya ga su da ɓarna, wata rana Aisha na suya taji wayan ta na ringing ta miƙe ta shiga ɗakin dan ta san ƙawar ta Mardiyya ce, da suka haɗu a islamiyyan da take zuwa, tana shiga ta ɗauki wayan tare da du bawa aikam taga ita ɗin ce, kafin ta sake latsa wayan suka ji gigitaccan ihu yaran nan, da salati ta fito ita ma Umma haka, aiko man suyan doyan nan ya zube ma Aisha babba wato yarinyar Umma ta ƙone sosai ta nata shure-shure, take ta rasu dan ta ƙone sosai ita ko ɗayan Aishan gefan jikinta ne ya ƙona, dan tare su kaje gurin suna rigima. Sunyi kuka kaman me, balle A'isha wacce take ganin kaman ita ce sanadi, a nayin sati 1 ita ma Aisha ƙarama ta bita dan tin wannan ƙunan bata samu lafiya ba, rayuwa haka taci gaba da tafiya a nan ne Umma taƙara haihuwa in da tahaifo tweens mata masu kama da ita,wanda suka ci Hajara da Maryam. tare da Aisha suke rainon yaran nan har Allah ya kawo ma Aisha ita ma ta haifa mace Ramlat wacce ita ma ita ta biyo kyau din ta dan Aisha akwai kyau ba tada haske amma kyau kam akwai shi. Lokacin da Tweens na da shekara 10 ita Ramlat ke da 7yr tare suke komai na rayuwa, rana daya aka wayi gari babu Aisha wanda mutuwarta ta girgiza kowa dan lau ta kwanta amma aka wayi gari bata (Rayuwa kenan Allah yasa mudace). Umma dukkan su ta haɗa take rainon su, amma sam ta dena sakin jiki da Ramlat bisa rashin sanin dalilin kowanne su, a haka suka taso bayan wasu shekaru aka kawo ma Abbuu kyautan Zainab da ga ƙaninsa me yara maza ganin ita maca ce yasa ya kaita gun yayansa, tare suka taso cikin ƙaunar junan su da natsuwa dan Abbuu mutum ne mai iya tarbiyyar ko yaro na rashin ji gun Ustaz ake kawoshi kuma da yaddan Allah ze shiryu, ya raine su cikin gata da walwala dan ya na da wa da ta sosai, dukkansu iyakansu secondry sch, amma islamiyya ko wacce sai da tayi N-Bayes ( Jsce na islamiyya). Cigaban labari Wayar ta ne ya ɗan yi ƙara a laman saƙo ya shigo, hakan yasa ta miƙe ta janyo jakkan ta dan du ba wa, a nan ne ta ga lokaci har 11:15pm yayi, wayar ta ƙiran Spark-4 irin nasu Maryam dan wayan su iri ɗaya ne, ganin MTN ne suka turo saƙon yasa ta koma ta kwanta tarasa me za ta yi dan haka takunna data tahau Facebook dan ganin abin da ke faruwa a duniya, a haka har barci ya dauke ta. 9:35pm Malam Ustaz yashigo gidan bayan sun gama karatun zaure da sukeyi sannan yakulle get din, sai da ya tabbatar ƙofon yaranshi na waje a ƙulle yake sannan ya shiga nasu ɗakin, bayan ya yi wanka yaci abinci suka zauna suna ɗan hira da Umma a nan ne take faɗa mai yadda sukai da Ramlat, sai da ya nisa sannan yace " Ai da ita an barta har muga abin da Allah zai nufa tin da ba ta da tsayayye" "Haka ne amma ni na fi so dukkan su a haɗa, a dai duba Malam, sun girma ma sha Allah" " To ai Umma sai idan mutum ya nemi da a neman mai cigiyan matan aure sai a duba a cikin ɗalibai masu natsuwa, ko ita Zainab da kika ga ni shi ya ganta ya yi magana shi ya sa, amma bamu san me Allah ze nufa ba " " Haka ne Malam Allah yasa mu da ce" ya amsa da. "ameen" sannan suka canza hiran. Washe gari da safe bayan ta kammala shiryawa ko breakfast ba ta yi ba ta huce ɗaya da ga cikin islamiyoyin Babanta dan koyarwa, ita kadai ke da ra'ayin koyarwa ban da sauran su dai sai aikin barcin kawai suka iya ita Zee kuma sarkin aiki. Sai 2pm aka tashi, uban yunwa ya ga ma gala baitar da ita dan dishi dishi take gani saboda ta na da ulcer, ta zo tsallaka titi kenan wata mota ta kusa ka ɗa ta, Allah yaso an ci uban birki, Idanuwanta a rintse tana an baton Allah ta kuma tsaya cak, har taji an bu ɗe motan da uban ƙarfi an fito. " Are u mad ? are u out of ur sense ?" cikin izza yarinyar da tafito da ga motan ta ke faɗa. " Ki ya ƙuri kuskur...." "shut-up, mtwwwwsssss, I hate poor people bcuz ba ku da hankali, da na bi ge ki da an ce laifi na ne, bayan ke ki ka shiga gaba na. Ramlat ganin ita ce da laifi yasa tayi ta ba ta haƙuri har ta hu ce, tsallakawa titin ta yi ta na jin ba ɗaɗi saboda wata banza ta za ge ta "Amma bakomai" abin da ta ce kenan ta na tafiya cikin natsuwarta wacce ya zama mata ɗabi'a. END Alƙalami daga Pretty Sk [5/29, 18:39] Pretty Sk: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION💪✍️ (J.A.W) Rubuyu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi. ✏️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 story and written by ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ page 3. RHYENO ESTATE MILLINIUM CITY Da sauri Abbas ya buɗe get din gidan, direct motan ta shiga ƙiran GLK, Budurwa ce mai ki manin 20yrs ta fito sanye da atamfa me golding wanda aka yi ma ta ɗinkin fitted gown me upon shoulder, sai gyalen kayan wanda ya ke hannunta, babban palourn ta shiga tana mai kwaɗa kiran sunan "Mom" jin shuru ya sa ta zauna ta na ɗan huci, ga ni ta yi hutar babban parlour ya ɗauke duk ka, take ma su colours su ka faraa bayyana cikin ƙawa da tsari kafin ta buɗe baki sauti me duka ya fara tashi na waƙan Happy birthday, Happy birthday, sai ga muta ne sun yo kan ta suna ihu, wasu na watsa mata ruwa wasu kuwa flowers suke watsawa, cikin jin daɗin ta miƙe ta na kallon su, ɗaya bayan ɗaya suke ta wishing na ta tare da bata kyaututtukan, Mom ta yi ma godiya dan ta san ita ce ta gayyato ma ta friends din ta da wasu ƙawayen Mom din sannan gashi ƴan gidan su sun haɗu duk kan su. Bayan ansha an ci aka watse, wanka ta shiga bayan ta fito tana kallon ɗakin nasu, gado biyu ne wanda do ga ye ne har can sama sannan akwai ta za ra sosai tsakanin ɗaya da ɗayan, sai glasses guda goma wanda suka ke wa ye bangon hagun ɗakin, ɗan madaidaicin guri ne a ta gefe da aka ƙawa tasl shi kaman ƙaramin parlour kujeru ne a za ga ye da shi, a can ta hangi mata kusan age-mate dinta su na ta hira, ɗaya daga cikin glass din gurin ta janyo sai ga shi ya buɗe irin cikin salon nan, take kayan sawa suka bayyana iri-ri, zaɓan ɗaya da ga cikin kayan gurin tayi, wani haɗaɗɗan riga da wando masu kyau ta sanya sannan ta nufe idan matan nan suke, su biyar ne zama ta yi kan one seater tana faɗin " Beauty ban gan ki ba da na fito class, har lap na leƙa amma banganki ba" wance ke latsa wayan ƙiran I-phone 16 wanda dukkansu shine a hannun su ta ce "Sorry Sis na so na kira na fa ɗa miki tare da costmate di na Haidar muka dawo shi ne ya kawo ni kuma da ma ina so na da wo da wuri saboda mu yi miki surprise." " Ai na go de mu ku sosai, Beasty hope kinyi videos koh" wacce ke cin choculate ta ɗago dan jin an kira ta, da kai ta amsa sannan ta ƙara da ce wa "Ai har na daura a kan sha fina na Instagram karki ga cikin 1h amma na samu like 500k " " Wow please Beasty, send to me now nima na ɗaura" cewan wata ita ma kafin Beasty ta yi magana aka buɗo ƙofan a ka shigo a tare su ka kalla su, mata 3 ne suka shi go, su na sanye da Uniform iri ɗaya na secondary school, kyawawa ne su ma kaman wa'innan su shidan, kuma kan su ku san ɗaya. " Sai yanzu kuka dawo? " Beauty ta faɗa ta na dauke kan ta akan su, cikin ɗan shaƙwaɓa ƙaramar su wanda ita ce ƙara acikin su tara 9 din ta ce " Hmmm Sis Beauty's school bus din ne yaɗan sa mu matsala " saura kuwa da sannu suka bi su kawai suna mai ƙara sawa ciki haraban ɗakin, da ya ke toilet huɗu ne kowan ne ya shiga ɗaya dan yin wanka, bayan sun fi to suka zauna suna acikin su suna hira sama sama. Misalin 8:20pm suka fu ta Main parlour dukkan su bayan ko wacce ta sanya kayan barci sannan ta ɗan ya fa gyale a kanta, zaune suke gaba ɗaya suna kallon wani American film me ɗaɗi wato Flash, duk da su na da TV a ɗakin su, a nan su ka ci abinci su na yi suna kallo, bayan wani lokaci sukaji horn din motoci, sun san su waye dan ha ka da sauri-sauri su ka ta shi suka koma part din su, suna shiga suka kulle ƙofan su na mai dan dariya ƙasa-ƙasa, dan basa son su ha ɗu da Pazars in sun shigo , wani babban abu Beasty ta dan na take wannan babban gadon ya fara rarrabe wa zuwa kashi 4 sai ya zama step by step gadon sai wani ɗaya a tsakiya, kowa nata tahau, sannan kandy wace tayi birthday ta kashe hutan ɗakin, take ta ji bell na ƙofan na ƙa ra ba yadda ta iya miƙewa ta yi ta kunna sannan ta buɗe ƙofan ta yi ta na kallon Momcy da ke san ye da hijab har ƙasa " Ku fto dukkan ku Pazars na ne man ku koma wasu sunyi barci ki tashe su " " Ga munan zuwa yanzu" abin da ta ce kenan ta na kulle ƙofan sannan ta juyo ta kalle su ta na ce wa " Mu hanzar ta su Pazars na kiran mu" jin haka su ka miƙe ko waccensu ta sanya dogon riga akan shigar kayan barcin sannan wasu suka yafa gyale wasu kuma suka futa ha ka, a tare suka gaishe da iyayensu maza su hudu wa'inda ke zaune a babban parlour, biyu suna sanye da manyan kayan biyu kuma suna sanye da suit da wando. da ga gefe guda iyayen su mata ne su ma su hudu suna sanye da hijabai.. END Alƙalami daga ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️ [5/30, 22:07] Pretty Sk: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK page 4. Pazar Q wato Baba Abdulqadir shi ne babba a cikin su kuma shi yaran shi uku ne maza biyu sai mace wato Baby amma na gaskiya Bilkisu shekaranta 16. Sai Pazar B wato Baba Abdulbaseed shi kuma yaran shi uku dukka mata Kandy (Khadijah) 21yrs take sai ƙannanta tweens Hasty da Husty ( Hassan da Husaina ) masu shekara 19yrs. Sai Pazar M, Baba Abdulmajeed shima yaran shi uku mata Hauwa'u wacce suke ce ma ta Beauty me shekara 21yrs sai Hajara (Beasty) ita kuma 20yrs sai autan su Karis wato Karima ita kuma 17yrs, Sai Auntan su Pazars wato Pazar R, Baba Abdulraheed me yara biyu shi ma mata Fancy Fatima kenan 20yr sai ƙanwarta Fadila suna ce ma ta Butter 17yrs. A tare suka gaishe su, suka amsa sai Pazar Q ya fa ra magana cikin natsuwa da taushi dan shi ya na da sauƙin kai sosai a cikin su be da damuwa gashi mutum ma ra son hayaniya. " Bilƙis, Karima da ke Fadila ku mai da hankali, SS3 zasu shi ga a mai da hankali sosai, nan da 1yr kuma kufara zuwa jami'a" Pazars Q ya kai nan yana kallon su cikin ƙaunar dukkan su, " Kuna dai kallo Bilƙis saboda ƙoƙarin ta jumping aka mata to ita ban jin ta amma ke Fadila kin fiya wasa." Pazar R yafaɗa yana ɗan zaro musu Idanu sanann yaƙara da cewa "Ku huce mun ga ma da ku, ku kuma kumai da hankali a kan rayuwan school" yana kaiwa nan su ukun daya nu na suka wuce part din su, da sauri-sauri kafin Pazar M da Pazar B ba su yi magana , suna shige wa, sai Pazar M ya ce yana kallon su shida din da ke zaune. " Ku kuma na samu labarin akwai mai zuwa makaranta da banza shiga to wlh nayi last warning a kan wannan ɗabi'ar in kunne yaji jiki ya tsira" yayi ƙwafa yana miƙewa ya huce part dinsa, sanan Pazar Q yace " Ku dai ki yaye kuma ku dage da karatu, Allah ya mu ku albarka ku je ku kwanta" kaman suna jira suka huce da sauri suka shige, sannan Pazar Q yakalli Pazar B yace " Na ga Abdulmajeed ba ya yanayi me daɗi hope komai nomal koh?" " Eh big bro Alhamdulillah, bako mai ƙasan haka yake ɗan zafi ne lokacin bayan lokaci" da ganan suka ɗanyi hira sannan kowa ya watse. ******* ******** ********** *********** " Zainab! Zainab!! zainab!!. " Ramlat da ke bubbuga ƙafan zainab wacce ke barci, buɗe idanunta ta yi ta kalli Ramlat ta fara magana cikin kasalar barcin " Ramlat lafiya? barci ya kamani, mene ne?" " Umma take kiran ki kuma ta ce ki zo yanzu" Ramlat na kaiwa nan ta fita ta bar ɗakin, ganin gari ya yi haske sosai tasan safiya tayi, a han kali ta shiga Parlourn Umma ta ƙafon da ke ciki na su ɗakin, ganin su Umma su na zaune ya sa ta zauna ta na kallon tween da ke ɗan sakan dariya kaɗan-aɗan, gaishe da Umma ta kuma yi dukda a al'adar su suna idar da subhi suke gaishe da iyayen na su, amsawa tayi sannan Umma taci ga ba da ce wa " Zainab an tsai da date din auran ku nan da wata 4mounth za ayi bikin ku, sannan gobe Muhsin ze fa ra zuwa zan ce. ke kuma Ramlat ba mu san me Allah ze nufa ba amma ke ma dai kishirya kawai " tana kaiwa nan suka mata sallama suka fita, suka shiga ɗakin su suka zazzauna kowa na kallon kowa, yau sam babu rawan kai atare da su sai jin bawani daɗi dan sun sa ba da juna ba sa son rabuwa, Ramlat dariya ta kwashe ta na tafa hannu ta ce " Waya ganni ranan bikin ku wayyo daɗi, kunsan Allah har rawa sai na koya saboda ku, ranan zan fara sanya gyale hehehehehe" babu wanda yakula ta sunata nasu harkokin kawai. **************** ***************** BADIKKO kan layin jajere wa ta ƴar budurwa na hango ta fito da ga wani gida sannan ta miƙa titi har ta shiga layin Sha'iskawa, wani ƙaramin gida ta shiga, sanye take da dogon riga sai babban mayafi wanda akai ta daura, choculate ce mai tsayin hanci ga ta doguwa siriri amma akwai hibs da breast ma sha Allah , ta shi ga gidan da sallama babu kowa a tsakar gidan dan ha ka ta buɗe baki ta fa ra kwalama kishiyar mamanta kira " Aunty! Aunty!!Aunty!!" ta faɗa da daddaɗan muryanta mai zaƙin gaske, wacce aka kira da Aunty ce ta fito ta na ta masifa da ƙaramin yaron na ta Umar don be san zuwa makaranta, sai da Umar me shekara 10 ya fita da ga gidan sannan Aunty ta kalle ta ta na faɗin " Uwar fitsara da rashin kunya an da wo kenan ? Me ye kuma na kiran na daga waje bansan iskanci fa " " Uhmm na dawo, na za ci babu kowa a gidan ne ai shi yasa na kwala kiran sunan ki" " Jeki huta ga wanke-wanke can ki yi sannan ki zo na ai keki kasuwa....." " Wlh ɗaya zanyi in ma kasuwan ko aiki, akan me ga Rabi da Radiya suna kwance" ta faɗa babu alamun wasa a fuskanta " Ramlat kenan hakanan zakiyi ko idan baban ku ya dawo hmmmm kinsan sauran" ta na faɗin haka ta koma cikin ɗakin, ita ma Ramlat ta bi ta ta shiga sanan ta shige ƙaramin ɗakin na su,, katifa biyu ne, ɗaya ta su Rabi ɗayan kuma ta Umar ce dan ita akan ƙaramin carpet ta ke kwanciya, ranta haɗe ta cire mayafin ta tu sa cikin gidan box din ta, sannan ta fita ta wanke kwanikan dan barci su Radiya keyi ma, kwanika kaman na mutane 15, sun ɓa ta kusan komai ta san Radiya ce ta yi girki da ma ta iya tara wanke-wanke, ruwa ta ja sannan ta zauna ta wanke su ta na gamawa ta koma ɗaki tayi kwanciyar ta dan ta huta ita ma, da ya ke akwai gajiya ajikint a ta ke barci ya ɗauke ta kan katifan Umar, barci me daɗi ya ɗau ke ta. Cikin barci ta ji saukan bulala a bayan ta, a firgi ce ta miƙe ta na ha ɗawa da ihu da kiran Allah, ganin Baba da bulala akan ta ta san yauma ta shiga uku, be saurara ma ta ba ya nata dukkan ta sai ya ya ma ta ruɗu-ruɗu tukun ya barta ta na ta hawaye dan har muryan ta ta tashe, da mutane amma babu wanda ya kwace ta agunsa kuma duk suna ji, ji tayi ya na ce wa " Ni na fita na sha wiya na ne mo kuɗin, dan an ce kije ce fane sai ki ƙi zuwa, yau ta kwana da yunwa karku ba ta abinci na, kun dai ji na faɗa muku," ta najin hakan tasan Aunty ce ta haɗa mata munafunci, tashi tayi ta je ta yi alwala ta gabatar da sallan magrib sannan ta shin fuɗa carpet din ta ta haukai ta kwanta, ko da ta ji sallan isha'i tashi ta yi ta gabatar sannan ta kwanta ta rufe da wani hijab din ta ta na jin duk duniyan ba ya ma ta daɗi sam, abubuwa da yawa su ke ya wo acikin kannta, muta ne biyu kawai take ke wa mahaifiya wacce ba ta taɓa ganin ta ba sai ƙawar ta wacce ta ɗauke ta tamkar yayarta ta jini. End of Part 1 alqalamin ᑭᖇᗴTTY ՏK [5/31, 17:27] Pretty Sk: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ بسم الله الر خمن الر حيم Part 2 Page 5 ********** ********* ********** Rhyeno Estate school bus ce ta yi parking sai ga su su uku sun fito suka shiga, Farida Karima da Bilkisu, motan ta ɗauka hanya zuwa makaranta, su na shiga kowacce ta zauna in da ta ke zama. Cikin haraban gidan kuwa tweens ne tsaye jikin mota ƙiran sport su na sanye da kaya iri ɗaya har ta gyalansu iri ɗaya ne da takalmi, ƙyawawa ne kuma farare ƙal haka dukkan su yaran gidan su ke, ana ganin su anga jini ɗaya kuma family ɗaya, Fancy ce ta fito da ɗauke da key a hannuta na basu haƙuri akan tsaida su da ta yi, ita ma sha Allah ɗinkin riga da pensil skirt ce jikin ta wanda atamfan ta haska ta, motan ta shiga ta yi mata key suka nufa Kasu dan su a can suke karatu, suma su Kandy, Beauty da Beasty na su motan suka hau suka nufa poly su a can suke karatun dan yanzu level 3 su ke. Gidan ya rage Pazars ne da matan su, Mom wato Maman Kandy tare su ka fito da Pazar B har mota ta raka shi sanan ta juya ta koma nabta part din, can sai ga Pazar M shima da Mamancy wato Maman su Hauwa'u shima motansa ya hau, yana sanye da kaya irin na Pazar M dansu sun fi sa ƙananan kaya, dan Pazar M shine minister of health shi kuma Pazar B minister of education. Bayan fitan su da kaman awa 1 Pazar Q da matar shi Aunty wacce ita ce maman Bilkisu, ita kaɗai ta haifa kuma ya aure ta ne bayan maman yaran shi maza ta rasu, shi ma Pazar R ya fito cikin ɗinkin zamani na manya kaya wanda ya sha uban aiki, matarsa Hajiya babta rakoshi ba saboda tana barci dan bata jin daɗi, tare suka fita suka shiga mota ɗaya suka nufa cikin gari gurin nasu business din. Bayan Aunty ta dawo zama ta yi tana kallo a Main parlour anan sauran suka same ta kowan ne cikin farin ciki suka gaisa da junan su, dan haka suke gaba ɗayan su cikin ƙaunar juna da rayuwa tare. Duk cikin su Aunty ita ce ƙarama dan su Mom sun girme ta, dukkan su ƙyawawa ne ma sha Allah, kuma farare sai dai kowa da kalan na sa haske, yadda mazan su ke ƙaunar junan su haka su ma matan suke, sannan duk ka yaran su ma haka su ka son juna. " Hajiya, wallahi kwanan zamu ne ma wasu ma su aiki kinga har 9am su Atika ba su zo ba." faɗin Aunty ta na mai da kanta ga T.V, " Zan mu su magana idan sukazo yau." cewan Mamancy ta na latsa waya kuma a take Atika da ƙanwar ta shatu sai wata zulai suka shigo, gaishe su su kayi sannan Hajiya ta musu faɗa a kan zuwa latti domin aikin gidan da yawa duk da na su shara ne da wanke-wanke kawai suna da me girki daban dan ita anan ta ke kwana. ********* *********** *********** Badikko Yau sai 12am ta dawo gida da ga gidan wata Hajiyan da take ma aiki ko da ta koma gida babu wanda ta kula ta shige ɗakin su ta zauna taci doya da kwai da aka ba ta a can gidan, ruwa ta sha sannan ta yi hamdala sai ta kwanta dan ta rantse a yau baza ta ɗaga ko tsinke a gidan ba, duk ihu Mamansu Rabi a banza dan Ramlat ko a jikin ta, ko da Rabi ta shigo a fusa ce da sauri Ramlat ta miƙe ta ci dam mara ta na ce wa " Wlh idan ki ka taɓa ni sai na rama kar ma ki fara dan kinsan bazan da ku miki ba " da ma inbdai rashin kunya da tsaurin ido ne Ramlat akwai ta dashi duk da Rabi ta bata shekara 3 dan ita Ramlat tana 19yrs ne. Fita Rabi ta yi sai ga Aunty ta shigo ta na ce wa " Ke ba ƴar iska, wlh Baban ku ze shigo za ki sani, bakya gani na da mutun ci, ko ruwa ba zaki fita ki ɗibo ba, uban wa ze ɗiba ruwan?." ta kai ƙarshen magana ta na shirin dukan Ramlat " Aunty ke ma kin sa ni kowa ya hanani shiga gidan sa ɗiban ruwa to ya kike so ayi?." " Shegen halin ki na dukan yaran mutane ba dole kowa ya hana ki ɗiban ruwa ba." " Kinsan haka shi ne za ki turani to?" ta faɗa ta na warware ɗan maran ta, kwantawa abin ta tana kuma ce wa " Ba ni ki ka sa Baba ya duka ba ai wlh sai nan da sati 1 zan ci gaba da miki aiki." Aunty rai ɓa ce ta fita haka Rabi ma, ko da baba ya dawo aka faɗa masa ƙarya da gaskiya sai ya dauko wannan bulalan ta sa ta gado ya nufa cikin ɗakin su, da ma ta ji ƙaran babur din shi, da sauri ya tsaya yana kallon ta tana rawar sanyi alaman zazzaɓi me zafi take yi. " Subuhanallah Ramlat me ke da munku.?" ya faɗa ya na aje bulalan a gefen ta, ɗagyar da buɗe idanuwan ta sannan ta ce....... END. Daga Alƙalamin Pretty Sk. https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ page 6 " Zazzaɓi ne kawai!", Na faɗa wa Mama amma ba ta ba ni magani ba kuma taita sani aiki, a haka naita lallaɓawa, ruwa ne na ce ma ta na gaji bazan iya ɗiba ba, shi ne na kwanta." kai ƙarshen maganan ta na hawaye, tsaki Baba ya ja sannan ya fi ce can sai ga su Aunty harda Umar, sun ji shuru ba ta fa ra ihun duka ba, shi ne su ka leƙo. " Lafiya ku kamin tsaye ha ka?." Ramlat ta faɗa ta na koma wa ta kwanta, sannan ta jero ma Aunty abin da ta ce ma Baba, ta ke ta haɗe fuska dan ta san halin Mijin na ta. " Wato ke gaki ƴar iska, lafiyan ki lau ki ke ƙaryan ciwo?." Aunty ta faɗa ta na kallon Ramlat da mamaki dan tasan halinta sarai, acikin kwanaki nan wani raini ta koya. Baba fita ya yi ya je ya kira wani me chemist , ko da ya iso, Baba ya futa bayan Ado me chemist ya biyo bayan shi, bayan Baba ya fito da ga ɗakin, can sai Ado me chemist ya fito, Baba ya biya shi kuɗin sa, sai ya ko ma gurin Ramlat din, su dai su Rabi na su ido, sun san halin Baba idan ɗan suna ciwo su na shan kula. Ramlat ta kalli Baban na ta wanda ke mata ya jikin. "Baba inajin yunwa, zan sha tea." bai ce komai ba ya kuma fi ta, dariya ta sanya har su Umar na ji, sai su ka shigo suna kallon ta. "Yarinyar nan kin riƙa" cewan Radiya ta na riƙe Kwankwaso, kafin Ramlat ta yi magana su kaji sallaman Baba cikin sauri ta ko ma ta kwanta ko da ya shigo ya umarci Radiya da ta ha ɗa ma ta tea din aiko ta haɗo ta ba ta. amsa ta yi ta kai baki da ƙyar, rabi ta sha sannan ta mi ƙa ma Umar sauran dan sun fi shiri yaron be da damuwa, amsa yayi ya koma ge fe ya na sha, a ranan Aunty ta sha faɗa haka su Rabi akan abin da su kayi ma Ramlat, ita dai ta na jin su hankalinta kwance. ******** ******* ********* *KIKINAU* "Maryan ɗan turamin Film ɗin nan na kalla" Maryam amsa wayan Ramlat ta yi ta tura ma ta wani Nigeria film ɗin da Maryam ta yi download dan sun ga poster kuma an ce ya yi daɗi sosai, Hajara ce ta shigo da sallama da ɗauke da babba plate a jewa ta yi ta na ce wa. "Bisimillah ga ma ra imani dukka na Annabi ya ce ya ƙoshi." suna jin ta faɗa ha ka su ka kalli plate ɗin, alkaki ne wanda yaji ruwan sugar ya ga ma jiƙa shi kuma yana ta walwal kwanin sha'awa, ta ke su ka sauka su ka fa ra ci, Zainab ma na shi go wa ta ɗauka biyu ta ce ya ishe ta dan ba ta wani cin sugar. " Mama ta yi?." Ramlat ta yi tambayan sai Hajara ta ba ta amsa " A'a Abbuu ne ya ka wo." " Gaskiya ya yi daɗi." Maryam ta faɗa ta na lasan ruwan zaƙin. ******** ********* *********** "Wallahi sai sun san ɓoni akan me dan na ba da shawara shi ke nan, aiko sun taɓo match, dole na san abin yi." " Ka din ga kai zuciyan ka ne sa Abdulmasheed kaji." " How? Hmmmmmm dole salon wasan ya sauya." wayan shi ya ci ro ya yi kira bu gu uku aka ɗauka " Gobe inaso na ganka sanann ka faɗa ma Babban yaya shima ya zo gobe nasan kai kaɗai ne zaka iya samun numbersa." ya na kaiwa nan ya kashe wayan. Baba Abdulqadir ya yi murmushi dan gobe ze ga yaran shi da ma so ya ke su dawo balle ma Babban yaya yana son ganin ya lafiyan shi ya ke, amma be san da munsu gashi Abdulmajeed ya kira su da ya ke shi ne ya san dole gobe za su dawo Nigeria. cikin faɗuwar gaba ta re da sauri-sauri ta nufi part din su bayan ta aje ma su Pazars drinks, yanda ta buɗe ƙofan da rufewan ya sa dukka su ƴan matan suka yi saurin ɗago wa, ko wacce da abin da ta ke yi amma kusan su hudu waya su ke latsawa " Baby lafiya kuwa?." cewan Hasty ta na du ba littafin karatunta, dukkansu kallon ta su ke yi dan ha ka ta buɗe baki a hankali ta ce. " Na zo da labari gu da biyu, bad one and good one." ta faɗa ta na ƙara sawa cikin su, zama ta yi kusa da Husty, sai Fancy ta ce. " Start with good one than bad din." " Ok, firstly tommorow Uncle ze dawooooo." yadda sautin kalman ƙarshe ya yi sai yai kaman a tare su ka ƙarasa cikin ihu da murna, su na ta hamdala sai Beasty ta ce " Ki ce mu shirya zamuga Uncle wayyo daɗi, dama banda ko sisi..." " Mayyan kuɗi kawai, ai sai mu ji bad din duk da ba ze tsora ta mu ba tin da munji maganar kuɗi." Kandy ta kai nan ta na mai da Idon ta ga Baby wacce annurin fuskarta ya ɗauke lokaci guda, dukkan su suka sassauta jin daɗin su su na sauraro ta " Pazar M ya umarci da a sanar mai shi ma ya zo goban nan." " Baby wa kenan?." Butter ta tambaya sai da baby ta ja dogon numfashi sannan ta furta kalmomi masu harɗe harshenta " BABBAN YAYA." daram, durum, dam, daan, zuciyoyin su ya bu ga sannan zu fa ya fa tsatstsa go mu su duk da A.C da ke aiki, duk cikin su Hasty ta fi kowa jin tsoro dan ta san case ɗin ta da Babban yaya. " Mun shiga uku, mun mutuuuu." kaman za tai kuka ta faɗa, sai Kandy ta ce " Me ya sa Pazar M, ze ma na ha ka, Allah ya soo munji, me ya ka mata mu yi toh?." " Two Hijjab gareni kawai , wayyo Allah." Hasty ta faɗa da muryan ƙasa-ƙasa, sai Beauty ta tari numfashi ta. " ke nima biyu gare ni ya kama ta mu je kasuwa amma banda kuɗi, wake da kuɗi a account dinsa?" dukkan su suka ce babu sai Kandy ta ce " I have 7k but ......" Ba ta ga ma magana ba Baby ta katse ta da ce wa " Mukira Uncle ya turo mana sai mu je amma yanzu 7pm yamma ya yi, ko an barmu sai dai mu ari motan Pazar Q." " Eh, ai muna da ke Baby, za kije ki riƙon mana Pazar. " " No Kandy wata ta je Pls " " Ke fa za ki tambaya, dan ko gun Pazar B ne tsaf ze ba ki key" a jiyan zuciya ta sauke sannan Besty ta ƙira Uncle Video call aikuwa cikin ɗan lokaci ya ɗa ga, da ya ke a system ne sai ta aje yadda zasu din ga ganinshi dukkansu, motsi wayan nashi ke ta yi sai kuma ya aje wayan ta ke fuskan shi mai kyau da ƙawa ya bayyana ya na mai sakin murmushi, fari ne ƙal kaman dukkan su, tweens ne kawai haske su be kai na su ba dan su hasken Mom su ka ɗauko, ga hancin su duk irin ɗaya mai tsayi dai-dai wa dai da, da an gansu an ga jini ɗaya sak ɗan dukkan su sun ɗauko fuskokin Pazars ne, fararere ƙwawawa ma su ka ma da shuwa-Arab, gaishe shi su ka yi, ya amsa da kai kawai ya na ta blushing abin shi ya na kallon ƙannan na shi ma su kama da juna wanda za'a iya za ta Babansu ɗaya ha ka Mama ɗaya, cikin murya shi mai daɗi da ɗan gurɓace wan yaran nasara ya fa ra magana " Gobe zan da wo Sister's." ganin babu wanda ta yi alaman farin ciki ya sa ya kuma magana sai suka ɗa ga kai alaman sunji sannan ya kuma magana. " Babban yaya koh?." a tare su ka ɗa ga mai kai sai ya yi murmushi ya san ƙannan na shi sam basa son Babban yaya ya da wo, Baby ta bu ɗe baki a hankali ta ce. "Uncle Plsssssss we need some money immediately." ya ri ga ya ma san dalilin kiran, a ta gefan shi aka mai magana dan ha ka ya kalle su ya na magana da sauri-sauri saboda ze koma bakin aiki. " Sister's am sorry kiran gaggawa amma karku damu, balallai Babban yaya ya dawo gobe ba sa bo da ga ba ɗaya Numbers din sa basa shiga na different countries, samun shi ze yi wahala sosai and zan tura muku kuɗin a account din Fatima sai ku raba." kai suka ɗaga sannan suka mai godiya ya kashe kiran. Walwala su ce ta da wo ta re da murna sai su kai hamdala su kaci ga ba da harkokin su tin da an ce Babban yaya balallai ya da wo gobe ba. ******* ********** ******* ********** *BADIKKO* Yau tin da ta wayi gari babu wanda ya shiga harkanta sa bo da abin da yafaru jiya, Aunty har kuka tayi saboda Baba in ranshi ya ɓaci sai haƙuri kawai, sukan su Rabi da yau bakinsu ya mutu, wanka ta fito sannan ta shirya ta sa kayanta tare da Hijjab, fitowa tayi ta kalli Aunty dake shara ta ce. "Mama ina kwana" harara ta maida ma ta sai ta fi ce abinta ta na murmushi tare da tina rayuwar baya. Labari ***** Baba mai suna Harun haifaffen Kaduna mazauni Kinkinau layin masallacin Ustaz sai kuma ya siya gida a badikko suka dawo sa bo da yafi kusa da gurin kasuwancinsa, ta yi missing ƙawarta aminiyar ta dan a gidan su take wuni, harta kowa na unguwan ya sheda ƙawancan su, tin ta na jaririya Mahaifiyata ta rasu a cewan Babanta, gurin Maman su Rabi ta taso cikin wahala da azaba sam basa raga mata ita da yaranta, ga shi ita yarinya ce me natsuwa da girmama na gabanta, ta na musu biyayya iyakar yinta, da ƙyar ta samu ta kammala junior level, islamayi kuwa a aji hudu ta bar zuwa, Mama ba ta bin Malamai amma tasan kan sharri babu ranan da ba zasu jamata duka ba shi kuma Baba baya bincike sai duka, shekara 3 kenan da dawo warsa unguwan sannan wata 7 kenan da ta fara zuwa aiki gidan wata Hajiya ta na ba ta 5k duk wata sai ta kaima Mama amma ko sisi bata ba ta. cikin kwanankin da be fi wata ɗayan ba ta fetse da zama ma ra kunya ba na gida ba har da ƴan layi da su ka tsane ta duk da sai wanda ya shiga gabanta ta ke mai raddi, Mama wanda a yanzu ta ke ce ma ta Aunty sai dai in agaban Baba ne. ta ɗaura ɗammaran nan da sati 3 wanda shine bikin su Radiya sai ta baƙan ta mu su kafin subar gidan, sunyi ma ta abubuwa da yawa, sharri babu wanda basa mata, a yanzu tsayinsu ɗaya dasu harma ta huce su, ta dai san a duku ba za ta bugu musu ba, yanzu ko ta zo da abinci ita da Umar kawai ke ci da kuwa su ta ke ka wo ma wa su ra ba, ta rantse kuɗin watannan idan an ba ta ba zata ba yarda ko sisi ba za ta sissiyan abubuwan buƙa ta ne, Mama in zata hana ta sai ta ce za ta faɗa ma Baban dan dama be san ta na zuwa ba rufa-rufa aka mai, ta yi shuru ne kawai sa bo da ba ta don su samu matsala da tini ta tona abin da ke faruwa. Cigaban labari A dai-dai ƙofan chemist ta tsaya dan ganin akwai wani aciki bayan ya fito ta shiga tana gaishe Ado, amsawa ya yi sannan ya miƙa ma ta 1k amsa ta yi ta mai godiya ta futa ta na jin daɗin dan kuɗin Alluran jiya ce sukai ra ba dai-dai da me chemist din ko wa ya dau 1k. ta na ta zance zuci harta shiga gidan Hajiyar domin yin aikinta. END *Daga alƙalamin Pretty Sk* [6/1, 15:56] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 story & written ------- ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ page 7 ************* ********** ************** ****************** KINKINAU yau ma kamar kullum ta dawo da ga islamiyya kenan ta shiga gida anan ta tadda Zainab da wani suna hira wato sabo saurayinta, dogo ne mai ɗan duhun fa ta, sai faman hira suke suna murmushi ƙara sawa ta yi ta gaishe shi aiko ya amsa cikin sakin fuska kaman ya san ta, sannan ta shige gida abinta " Masha Allah ashe ƙanwarki ta fiki kyau duk da tana sanya da niƙaf amma masha Allah kawai." Muhsin ya yi maganan da si gan wasa dan ha ka Zainab ta ce " Uhmm na ji ai da ma nasan ni banda kyau." sai ta miƙe tsaye ta na turo baki duk cikin wa sa " Ha ba gimbiya, ita ta isa ta fiki kyau wasa na keyi na janye kalman, My haƙarƙari zauna abin ki" sai suka kwashe da dariya dukkan su, ta zauna suka ci ga ba da hiran su ita kuma Ramlat ta shiga ɗakin su. **** " Sis gaskiya Zainab ta yi sa'a nasan wanda nagan ta dashi a wajen nan." Ramlat ta faɗa ba ya ta cire hijab din ta sai Hajara ta ce " A ina kika san shi?." " ya na kawo wasu yara islamiyyan mu, gaskiya mutum ne mai kyauta da sakin fuska ba shida da mu wa." " Ma sha Allah ha ka ake so, naso nima na ganshi amma akwai wata ran ai ba zan fita yau ba." " Hmmmmmm ai Yaya Muhammad da Yaya Usman sun fishi kyau." Zainab ta faɗa a lokacin da take shigo wa, sai maryam ta ce " Uhmmm bawani nan Usman fa be da tsayi." sai suka kwashe da dariya sannan Zainab ta kuma magana ta na kallon Ramlat " Ramlat ta shi ki faɗa mana wane ne yafi kyau aciki tin da duk kin san su." sai su ka mai da hankali akan ta sai ta ce " Yaya Muhammad na Hajara shi be da damuwa, salihin ba wa ga kyauta, toh na baki 70%, shikuma na Maryam ya shin 20% zan bashi mutum sai uban kishin tsiya....." "Tab ana nuna min wariya anan gurin amma ai fari ne dai." Maryam ta faɗa ta na dan hararan Ramlat " Eh amma kinsan dai halin shi ga faɗa, ba gaira ba dalili za kisha fa ma Husaina." cewan Hajara "Uhm sai Yaya Muhsin shi kuma na ba shi 95%...." " Iyyema yarin yar nan ba bu mai 100%?." "Gaskiya babu ana wa result din sis Hajara" " To Allah Ubangijin ya baki mai 100% ƴar autan mu." " Ameen Zainabu tahhhh." " Ramlat ba ma kunya , ah to ya yi ma na." Hajara ta miƙe ta fita dan du ba girki, su kuma su ka ci gaba da hiran su kwanin sha'awa. ********* ************* ************* Babu wanda ya fita agidan yau sa bo da suna shirin tarban Uncle, misalin 1:30 Uncle ya da wo kar kuso kuga yadda familyn ke nu na mai ƙauna da kulawa, wanka ya yi sannan ya fito su ja haɗu a daining danyin lunch, su 18 ne ko wa da yalwataccan murmushi, Uncle mutum ne mai wa sa da dariya, do go ne mai cikan haiba da kamala be san abubuwa biyu a rayuwan shi, rashin kunya da tsiwa shi yasa su ke shira da ƙannan na shi duk da akwai ma su wannan halin "Ya maganar BABBAN YAYA." faɗin Pazar M ya na shan ruwan kwakwa, sai da hantar ƴam matan suka, dan jin sunann Babban yaya, sai Uncle ya ce " har yanzu duk ka numbers din ba sa tafiya kuma last call dimu ya ce china za shi." " Okh ai wallahi idan ya dawo gidan nan, ya shigo kenan ba shi ba barin ƙasar nan, kusan 2yrs be zo ba ba shi da aiki sai ya wo zuwa neman magani, ni fa ba yadda da wannan yaron da suke ta re na ke ba kawai shaƙa tawa su ke zuwa ƙasashen duniya." Pazar B ya kai magana ya na jan tsaki sai Pazar Q ya ce " Wai Adamsi?." " Eh mana shi, basu da na yi sai ya wo hmmmm." " Pazar M Insha Allah za mu sa mu numbers din shi. " Shike nan Allah ya sa." wayan Uncle ne yahau Ringing ganin new number ku ma True-caller be yi identifying number ba ya sa be ɗauka ba, sai da ta katse har sau biyu, dan abinci suke ci ne, su na ga ma cin lunch, su ka ko ma Main parlour suna hiran su, Baby sai labari take ba shi ya na ta dariya, ya na son familyn shi, su Pazars kallo su keyi a babban T.V su kuma Momcy na su hiran suke na manyan muta ne,, take aka fara haska labarin da ya girgiza Nigeria a satin nan, Video ne wanda aka saki yanzu a Social Media, hakan ya sa kowa na Parlour ido ya koma kan T.V dan jin cikakken rahoton abin da kunnuwan su su ka jiyo, cikin majigin TVn wani mutum ne ke zaune kan wani dogon gujera, ya na san ye da baƙaƙen kaya wanda ko ina na jikin sa a rufe ya ke harta kwayan idon shi ya sa glass magana ya fara yi ciki wani kalan murya mai amo da cika kunnan me sauraro. " Ƴaku mutanen Nigeria barkan ku, ni ne wannan ɓoyayyen masheƙi wanda ku kafi sani da RASH masheƙi, a yau ma zan dauki ran wannan shahararren dan kasuwan nan mai suna Ibrahim Sani Greto ...." "Ibrahim greto kuma, wai ni waye wannan ɗan Iskan yaron ne, kaman babu hukuma a ƙasar na, ha ka last week ya nuna ya kashe wani Doctor a kebbi state" cewan Pazar Q ya na jin ba bu daɗi har ransa, ai kafin ya maida idon shi ga T.V RASH ya yan ka Ibrahim Sani Greto, sai jini ke zu bowa da ga jikinshi, salati su ka hau yi dukkan su suna ta duba wayoyin su ganin ko ina an haska wannan mugun videon dan direct ne, kuma masheƙin yakan kashe kowa sannan ya datsi tashoshin TV ya musu ƙurar, daganan sai muta ne ɗauka a sa me dukka Media sai abin ya yaɗu. " RASH! RASH!! shi ne babban matsala muta ne a yanzu, kashe mutum a gunsa ba bu wahala, gashi sai bincike akeyi amma ko ma kama ɗaya ba'a samu ba, ya kashe babban ɗan kasuwan na Nigeria wanda ya ke zaune a Abuja wato Ibarahim Sani, kuma kafin shi ya kashe wasu, shin wai wanene RASH? RASH, RASH masheƙi sunan dake ta yawo kenan a media, hankalin mutane da ya wa ya na ta she saboda........" kashe T.V Aunty ta yi ba tare da me rahoton ya kammala zan can ba, ce wa ta yi " Wallahi Nigeria babu tsaro ko kaɗan, wannan ai ba rayuwa bane." ta faɗa ta na zama kusa da Pazar Q sai shima yabce " Mudai mu dage da Addu'a kuma Allah ya tona asirin mugun yaron nan RASH masheƙi." suka amsa da Amin. Number da zu ne ya ƙara shigowa alaman Ringing sai Uncle ya latsa accepting ta re dayin sallama shuru har sai da yayi sau uku, sannan ya latsa wayan ya koma a speaker, a karo na hudu yana yin sallama da re da niyyan yanzu ze kashe kiran sai ya ji an ce " Wa'alaikumul salam, da Uncle Aliyu Haidar na ke magana?." " Eh ni ne." " 1 minute." abin da aka ce kenan sannan ya ji wani ya amsa ya wan ya fara magana, jin muryan ya sa dukkan su, suka natsu sannan Uncle ya ƙara volume don su ji da kyau. " Nan da awa biyu da rani zan zo gida, na samu labarin Pazars na ne mana ka ce mu su inan ta fe." kafin Uncle ya yi magana ya kashe wayan, ta ke ya kira layin sai ya ji Switch Up, murmushi ya yi sanan ya ce " Babban yaya ya na Nigeria ashe, sai ashirya tarban shi anjima ze dawo." Pazars, Uncle da su Mum sai murna suke yi suna jin daɗi banda ƴan mata 8 dinnan, ɗaya bayan ɗaya suka shige ɗakinsu da yake jiya Uncle yasa musu five hundred thousand, dan haka suka fito ko wacce ta shigan mutum ci, sanan Baby ta ɗau musu permision akan zasu kasuwa yanzu zasu dawo, Pazar Q ya basu key ya ce Fancy ta yi tuƙin dan ya fi yadda da na ta akan na Kandy dan ita akwai gudu da ganganci, cikin motan su ka shiga dircet wani Super market, suka shiga ga ba ɗayan su, yeard din hijabai suka siya da uban yawa ɗin kakkku, sai jallabiyoyi da niƙaf sanan suka koma mota kusan kuɗin ya ƙare dan haka Fancy ta ce " Nidai inason 10k dan yanzu school za muje na amsa wasu takaddu." " Babban yaya bala'i niwai ma ya zamuyi kunsan shi da yazo in ya shigo room din mu sunan mu sorry, muje dan ni gidan su ƙawata zaku kaini na amsa text books dinbta, akwai ƙura fa dan kunsan sauran." cewan beauty, sai Hasty ta ce " Ya maganar hadda, yanzu sai ya ce sai munyi tilawa in ya zo, na manta yaushe rabon da na yi karatun Alkur'ani wayyo ni wayyo Allah na." ta faɗa Kaman ta yi kuka, motan ne ta tashi ta fara ta fiya sai suka yi playing Qur'an suna saurara sai mistake suke yi dan inbaka maraja'a to hadda na gudu wa. Baby, karis da Butter hankalinsu akwance sa bo da su suna zuwa islamiyya kuma basu hada tahafiz ba suna maraja'a sosai, Poly suka fa ra zuwa su Kandy suka shiga su ka ga ma komai sannan aka nufa Kasu nan ma masu case suka gama, sai suka je gidan ƙawar Hasty ta'ara abubuwa da yawa, suna komawa gida suka ƙyara ɗakin na su, su ka ɓoɓɓoye ƙananun kayan su, suka sha hijabai suka zauna kowa taɗau ƙur'ani suna ta maraja'a banda Karis dan ita case din ta a ta kaddun boko ne ɗauka ta yi tanata bita, baby ku wa hadisai ta dauko tanata hadda ce wa abinta dan ita akwai kwanya sosai.. End. Daga Alƙalamin Pretty Sk. [6/4, 22:08] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ Page 8 **************** ********************** RHYENO ESTATE Sanye ya ke cikin kayan police wanda ya ƙara bai ya na matuƙar kyaunsa, ya na da duhun fata, choculate colour ne amma me ƙyalli, dogo ne kaman Uncle, jikinsa duk a murɗe ya ke wanda ka na ganin sa suffar sa ta ƙar faffan namiji za ka ga ni, kyakkyawa ne a jikin farko, ya na da dogon hanci da man yan eyes, ya na da faɗi sosai ga dam tsen sa, sai ma sha Allan kawai, cikin farin ciki ƴan gidan suka mai tarba mai kyau kuma ta musam man kaman sun san da zuwan sa " Uhmmmm ZAKI mai three stars wato ASP a yanzu, kana zamanin ka, gashi dai ka sake ziyaran dole tin da an turo ka Kaduna." cewan Aunty ta na miƙa mai abincin da ta zuba a plate, muryan shi mai amo da cika kunni, ba na ihu ba amma mai sautin daɗi. " Auntyna kenan abin sai addu'a, dan kwana biyu kawai zanyi na koma, babban case ne ya kawo nan din." " Ma sha Allah, to Allah ya taimaka." ya amsa da ameen, sai ga su Baby da Karis cikin ladabi suka gaishe shi sannan suka ko ma ɗakinsu dan da ma sun leƙo ne suka shin Boss ne ya iso, sai suka ga ƙanin Aunty ne da ga Abuja ya zo wato ASP Umar wanda ake kira da Zaki dan shi akwai ƙarfi da jarunta, suna shiga ɗakin na su su ka sanar ma sauran da cewa Zaki ne ya zo, aikam suka je suka gaishe shi dukkan su sannan suka koma ɗaki suna jin Aunty na mai albishir da ce wa " Ka yi sa'a yau Babban yaya ze shigo." dauke farin ciki a fuskan sa da annurin, sai ya ce "Alhamdulillah ki ce yau zamu haɗu?." ta ko ɗa ga mai kai. anan Uncle ya sauko ɗa ga part dinsa dan anan Uncle ze sauka. " ya ka mata ka ma na two weeks mana." Uncle ya faɗa ya na kallon Aunty dan ta sa baki, aiko ta sa " haka ne Zaki ka mana sati biyu mana kaji." " Hmmm Aunty ba zaku ga ne ba, two days kawai zanyi, in da daman na dawo zan dawo domin ni yanzu Kaduna to Abuja zan din ga shiga no excuse, wani babban case ne kuma akwai abubuwan yi anan ne shi ya sa na zo, ina zaman zama na aka ɗauramin wannan bala'in dan basan ta in da zan fa ra ba." Ya kai ƙarshen ya na sauya yana yin fuskan shi zuwa ya na yin da muwa. "Subuhanallah ka ce case din babba ne?." " Aliyu sosai, yau ka dawo amma nasan ka sa mu labarin masheƙi wato RASH..... " " Badai wan da ya yi kisan ɗazu ba?." Aunty ta faɗa ta na zaro Idanuwa dan wuni yau ba ta hau online ba dan na T.V kawai ta ga ni amma hankalinta ya tashi sosai " Shine Aunty, mutum kaman aljani, Ba'a ga ne harin sa, kisa na shida kenan amma biyu ya sa ke a media kuma dukkan su shahararrun muta ne ma su ji da kuɗi a Nigeria." " Gaskiya an ba ka aiki Zaki Allah ya taimaka." " To Ameen, Allah ya tsare mana kai." abinda Aunty ta faɗa kenan ta miƙa dan fyuta compound, su ma miƙewa su kayi suka nufi Compound din dan mota ta shigo gidan na su sun san Baban yaya ne, ga ba ɗaya jin mota ta shigo ya sa fito dukka mutanan gidan su ka dan tarban shi, dai-dai nan Pazars su ma suka fito daga ƙaramin Parlour dan a can suka wuni ko da Zaki ya iso a can ya je ya gaidasu ganin suna tattaunawa mai mahimmanci ya sa ya fita ba suyi hira ba. Bayan motan ta fa ka sannan wanda ke mazaunin Driver ya buɗe ya fito, saurayi ne mai kimanin shekaru 26 ya bayyana, ya na sanye da ƙananan kaya masu tsaɗan gaske choculate colour ne shima kaman Zaki, sai dai be kai Zaki tsa yi ba dai-dai ya ke. Babu in da Idanuwan shi su ka fa ra saukan sai kan bugun nunfashin shi wato Kandy, murmushi mai sanyi da ɗauke da ma'anoni iri-iri, da isar da saƙon ƙauna ke tasiri a cikin sa, suka sakar ma junansu na wasu seconi, sannan ya kalla su Pazars ya na faɗin "Ina yinin ku Pazars" su ka ɗa ga mai hannu, take ya danna Remote din hannu shi sai motan ta buɗe ga ba ɗaya, Wheelchair ya fara fito wa dashi ya ajiye a dai-dai ƙofan motan me na baya,, bayan wani ɗan lokaci fararen ƙafansa suka fa ta bayya na, ƙafa wanda za ka za ci ko ƙasa ba ya ta kawa, ƙafa irin na jarirai mai kyau gashi fari ƙal har ta farcansa farare ne me ɗauke da kwantaccen jan jini sai a tafin ƙafan na sa sai ya ba da style, sai gangan jikin sa shi ma su ma bayyana bayan ɗan lokaci ma sha Allah, duk hasken matan gurin da mazan sai na ga asha baƙaƙene agun wanda ya fito, fari ne ƙal wanda ya haɗu da jajaja, fuskan sa mai ɗauke da annuri da haiba sannan ga kamala ya bayya na, hannu ya sa ya cire glass din da ke fuskansa ta ke kwayan idonsa ya fito fari ƙal, cikin kuma ɓaƙi huluk, sai gemu wanda duk wanda ya gani yasan yabna shan gyara na zamani, ga hanci dai sak irin na Familyn sa, Allah ya yi mai kyau kwarjini da kamala, manya kaya ne jikin sa wanda suka ƙa ra bayyana tsayuwan gangan jikinsa, murmushi yake yi mai sanyi wanda har dimple dinsa suka motsa, kallon su ya ke dukkansu cike da so da ƙauna ma ra misal tuwa, kaman ya ta lo dan ta fiya sai dai me abin tausayi wannan Wheelchair din ya samu yahau da taima kon jikin motan da ya da fa, da ya ke wheelchair din me ta fiya da kanta ne aiko ya danna abu ajikin keken ya nufe su inda su ke tsatstsaye, ta ke Baby hawaye ya zubo mata dan ganin yayan su da sauri suka nufe sa suna ta jin daɗin kaman ba su su ne suke ta da hankalin su sa bo da ze dawo ba. dukka matan hawaye suke yi 2yrs ba wasa ba da ma tun can ba wani zama ya ke a gidan ba, da ya dawo kwana biyu yake yi zuwa uku za'a ne me shi a rasa a gidan ya huce shida jagoran sa kuma abokinsa Adamsi. babu abin da ya furta har sai da suka shiga Main parlour sanann ya gaida su pazars cikin girmamawa, ha ka su Momcy, sannan ƙananan shi suka gaisheshi wa inda suka sanya hijabai dukkan su kwanin sha'awa, "Boss ya dawo ai komai dole muga sauyi dan ansan sauran." Hajiya ta faɗa ta na kallon ƴaran na su, daya ke sunga ne me ta ke nufi sai suka yi murmushi kawai. (U are welcome Boss) ************* *************** "In ma ku faɗa gaskiya ko a'a banda damuwa, domin ni ban jira, take zan ɗa na kunamata sai in fasa kwanyar ka." bindiga ta sai akan wani wanda ya ke cikin cell, sannan ta janye ta na coka bindigan a jikin pocket din wandon jeans dinta, black wanda ya kwanta ma ta, sai riga me butura white da ta sa sai kanta wanda ta sanye p-cap sai bindin gashinta wanda tayi mai donut ya fito da ƙasan cap din, ba fara ɓa ce amma duhun ta me kyau ne bima'ana choculate colour ce mai matukar kyau, kyakkyawar gaske amma sam fuskarta babu alaman dariya a ɗaure ta ke amma kyau wune zalla a fuskan, cikakkiyar mace ce, son kowa ƙin wanda ya rasa inji ba haushe, fita ta yi da ga cikin cell din ta na duba agogon da ke tsintsiyar hannunta na Apple. "Gobe da safe Zaki ze shigo ku tabbatar kun haɗa komai." ta faɗa ta na kallon mataimakinta sajent Nura, kafin ya amsa ta ma fice sai kuma ta dawo ta na faɗin " Ku saki ɓawaron babur din can, ku goge komai dan gane da shi." " Madam mashin fa ya sa ce badan Allah ya sa an kama shi ba fa......" " Umarni na ba ka Nura." tana kaiwa nan ta fice motarta ta hau taɗau hanya zuwa gidansu, a take ya cika umarnin ta ɗan yasan Madam komai tayi akwai dalilin yinsa, buɗe cell din ya yi ya fito da wani sannan ya sallame shi. Ita kuwa tafiya take yi a motan ta na jin ba daɗi a ranta sa bo da rayuwa ta yi wahala a Nigeria, ta fahimci ba shine ya sa ci mashin ɗin ba sahun ɓarawo ya ta ka, horn tayi ta ke aka buɗe mata get ta shi gidan nasu mai kyau da tsari, parking lot ta je ta yi parking ta fito, waya da system kawai ta ɗauka ta shiga Parlourn nasu, babu kowa dan haka ta shige part din ta, wanka ta yi sannan ta yi sallan magrib, ta ɗanyi karatu Alqur'ani har aka kira sallan isha'i sai da ta gabatar sanann ta fita palourn anan ne ta tadda Mahaifiyarsu Hajiya da yayan nin ta twin maza Yusuf da Yunus masu kama ɗaya dan ita da take ƙanwar su da ƙyar ta ke banbance su saboda Yunus yafi ɗan sakin mata fuska akan Yusuf, su Lawyers masu zaman kansu, shi ya sa abubuwa da yawa ke ma ta sauƙi sa bo da su dan kowani case ta ka wo gunsu sai inda ƙarfi su ya ƙare, suna kama sosai dan mahaifin sa suka biyi amma mahaifiyar su ta nada haske ita, su uku kawai ta haifa, Mahaifin su yarasu shekarun baya, su mazan sune suka za ma mata uba. za ma ta yi cikin su suna ta hira cikin nishaɗi da walwala abin su. End Daga Alƙalamin Pretty Sk ✏️💪. [6/9, 07:44] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ ‏﴿ رَبَّنَا هَبْ لَنَا مِنْ أَزْوَاجِنَا وَذُرِّيَّاتِنَا قُرَّةَ أَعْيُنٍ وَاجْعَلْنَا لِلْمُتَّقِينَ إِمَامًا﴾ ♥️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ page 9 ********** ***************** BADIKKO Kwance take akan katifar Umar ta na shan choculate mai suna cash, murmushi ta saki dan yau kaɗai ta san ta ƙuntata ma su Rabi balle Mama yau ta shaƙa abin haushi, ta na jin ƙaran mashin ɗin Baba tayi sauri ta janyo hijab ta rufe jikinta, aiko ya na sauka a mashin din gurinta ya nufo bayan sun gaisa da su Mama a parlour, dubanta ya yi ta ce mai da sauƙi sai ya fita ta, da ya ke su Radiya na parlour haka suka kuma gaishe sa dan ɗazu bai amsa ba, yanzu dai ya amsa amma sama-sama, sai ya shige ɗakinsa. Da ƙyar Baba ya sauka daga fushin da yake yi, a haka suka kwana dai badan ya haƙura ba, ko da gari ya waye ya bar gidan babu wanda ya shiga harkanta ita ma tana ta harkokinta, sannan ta fice, misalin 2:30 ta dawo, mama kallo take yi a madaidaiciyarT.V dake Parlour, 2k ta miƙa mata tana cewa "Hajiya ta kore ni daga aiki sannan ta biya ni kuɗin aikin shine nace bara na baki 2k na dau 3k zanyi abubuwan yi da shi.". Kaman ba za ta amsa ba sai ta amsa kuma ta ajiye a gefanta, Ramlat kallon Radiya tayi wacce ke ɗinki a keken ɗinkinsu, take jikinta ya yi sanyi da yanayin nasu, ko banza ƴan uwanta ne ta daure tayi haƙuri wata rana sai labari, hakuri ta basu da har sun share ta ganin abin ya kusa kaita bango yasa Mama tace "To shike nan ya huce." Daga haka sukai alƙawarin daina musguna ma rayuwarta dan a yanzu sun san ita ma tsaf za ta iya musu makirci wanda yafi na su, to menene amfanin sa kowa ya haƙura, haka Mama suka ba ya haƙuri akan duk abubuwan dasu kamata, da yake Ramlah yarinya ce mai haƙuri da sauƙin kai, sai komai ya wuce a gunta kuma da zuciya ɗaya. ************* ************** Ko bayan sun gama gaishesa da kai dai ya amsa musu fuskan nan tasa yadda dai ta ke kullum, a hankali dukan su suka silale zuwa ɗakin su, bayan sun wuce ya kalli Uncle da idanuwansa farare ƙal ya najin soyayyan ƙaninsa na ƙara ambaliya a cikin jikinsa " Aliyu ya aikin na ka. " " Alhamdulillah Babban yaya, nai ta kiran numbers din ka amma ba sa shiga sam." sai da ya saki ɗan murmushi sannan ya ce "Haka ne sai haƙuri da ni bara na ƙarasa ɗayan Parlour na kuma gaida su Pazars." Ya kai nan ya na kunna kekensa ta nufi ɗayan parlour, da ido Uncle ya bisa, yana mai jin tausayin yayansa, har ƙwalla sai da ya share ya na tuna lokacin da yake tafiya da ƙafafunsa lau. Ganin idan ya cigaba da tinanin zai sa ya tuna tashin hankalin da suka shiga a lokacin sai ya nufi part dinsa dan Zaki nacan na jiran sa, yazo zai hau stairs sai ya dawo yabi bayan Babban yaya dan rakasa duk da Adamsi na bayansa dan ya shigo yanzu. Gaishe su ya ƙara yi suka amsa, Pazar Q farin ciki fal zuciyansa dan ganin Babban yaya, yana cikin ƙoshin lafiya, yana matuƙar kawaici rashinsa a kusa da shi, gashi ya na matuƙar son Babban yaya, fiye da sauran yaran gidan amma be taɓa nuna wa ba ko damuwan sa akan wasu abubuwan ba ya nuna wa. "Allah ya dawo mana da kai cikin amiincin sa, ka sani mun gaji da yawon ka da sunan ka na neman maganin ƙafafuwan ka, ha ka Allah ya so ba kada wata duba ra ma guje ma Allah, idan ya nufa za ka sa mu lafiya In sha Allah za ka samu Babban yaya, sannan wannan mutumin." Pazar M ya nuna Adamsi sannan ya cigaba da ce wa " Ya kasa ba ka sharawa a kan ka na tsu guri ɗaya, yawan nan be da amfani a ƙalla kusan 8yrs ba ka natsuwa guri ɗaya, har kwanda da karutu ne amma yan zu ba bu fa, kai kam sai biye mai ka ke yi kaman bindi in ya ce muje sai dai ka bishi kaman bindi, hakan ya ishe ni." Murmushi suka yi dukkan su sanan Pazar B ya da sa " Shuraim me yasa ka ke yawan can za numbers nea shekarun nan?. ba a samun ka sai dai in ka so ka nemi mutum?." jin tambayan ya yi kaman a sama sai ya kalli Adamsi, aiko su na haɗa ido sai Adamsi ya nufa ƙofa da waya a kunne ya na amsa kiran ƙarya kawai so ya ke ya gudu dan be san me ze idan sun tambaya sha, "Hello Sunusi, Alhamdulillah" ya furta ta na fice wa daga parlour, Shuraim ya girgiza kansa sannan ya ce " Pazar babu dalili." abin da ya ce kenan sai shuru ya ra tsa babban parlour na wasu lokaci kafin Pazar Q ya katse shurun "Shuraim akwai muhummin abin da ya sa Abdulmajeed ya nemi da ku da wo dan haka gobe zamu tattau na ku je ku kwanta." " To Dad." da ga haka ya mu su sallama ya fita shi ma Uncle ya bishi har ze huce part ɗinsa sai ya koma ya juya ya nufi part din ladies, da ma sun san sai ya shigo kuma jiran na shi suke yi dan ha ka ya na Knowking Beasty ta je ta buɗe mai ya shigo shi kuma Haidar ya wuce dan ya san operation duty ze yi, dai-dai ta tsayuwan keken na sa ya yi, sai ya ga dukkan su sun ƙaramai girma bakaman da ba, yana son su dukkansu ya na ƙaunar su fiye da tinanin su amma sam ba ya nuna musu sa bo da in kowa ya nuna mu su kulawa akwai matsala. Gasishe suka yi ko wacce jikinta a sanyaya sai ya kalli Fancy ba tare da ya amsa gaisuwa ba ya ce " Fatima a ina kika sa mu five hundre thousand jiya? misalin 9:37pm." Ras ga ban ta ya faɗi haka na sauran ma cikin in Inan da ya shiga bakinta ta fa ra magana '' Un..c..le... Uncle, da ma...ya turo ma na ......" " For What?." ya katse da da ɗan zafi-zafi, ya sani da cewan Uncle ne ya tura musu sa bo da komai suke ya na sa ne amma so ya ke yaji me zasu ce, shima abin da duk su ka siya ya sani har da sauran ƴan gidan komai ya sani sannan duk rayuwar da suke yi ya sani komai da komai, cikin rawar murya ta kuma magana "Dukkan mu ne ya turo ma na sa bo da akwai abin da za muyi dashi." shuru ya ratsa duk abubuwan da suka siya ya sani sai ya ba sar, keken nasa ya murɗa har gaban glass din kayansu sannan ya matsa gurin dressing mirrow ya na ƙare ma lotions da turarukan gurin kallo ya bi da kayan gurin, ma sha Allah kaya ne shafa ne kaman me sun jeru sun tsaru sosai yadda kasan gurin saidai su dan kusan komai daban-daban, mai ɗaya ya dauka ya na dubawa ganin an sa Whiting Lotion for 3days only. " Wa ke bleaching acikin ku?." ya tambaye su yan na riƙe da roban man, yasan babu wacce take yi dan duk hasken sune amma ya tambaya fuskansa ya na ɗaure dan ko murmushi ba ya musu to ina ma su ke ganin shi sai dai wa Uncle shi ne za ka ga ya na murmushi. " Babban yaya wlh a siyyan kayan make-up ne mu ka haɗo da shi kuma sau biyu na shafa na daina." har Idon ta ya ciko da kwalla da ma ita akwai saurin kuka " Husaina ba ha waye na ce abin ba." sannan ya ya dawo in da suke zaune dukkansu, har ran shi ya na ƙaunar dukkan su wallahi balle ma Baby wace kamansu tafi ɓaci duk da ba Maman su ɗaya ba. ya umarci kowa ya kawo mai ta kaddun su na makaranta duk suka kawo cikin ikon Allah duk suka cinye tambayoyin, sai da s kazo karatun Alkur'ani nanfa ido yaraina fata gun Beasty, Beauty, kandy,Hasty da Husty dan ba sa maraja'a, aiko sun sha faɗa sosai da umarnin zuwa gobe su tabbatar haddan izu goma ta dawo, koda ya futa babu wacce ta kwanta da wuri suka da ge da karatu ga shi ya yi season phone's din su. Part dinsa ne na farko dan haka ya shiga ya sa mu abokinsa Adamsi ya gyara ko ina kuma ya shigo musu da kayayyakin da suka zo da shi, zama ya yi kan lafiyayyen sopa, jikin shi be sann wahala ko kaɗan irin ƴan ga tan nan ne masu wuni a A.C, za ma ya yi tare da ɗaukan system ya shiga operating cikin matuƙar kwarewa. sai 2am yayi barci dan tini Adam ya kwanta a kan makeken bed din Shuraim... * Koda yashiga nasa party din ganin Zaki na kwance ya ce " Ya futan ba ko sai gobe?." " Ai bar shi kawai dama wani shop na gani akan babban titi, na hango wani snacks ya burgeni a cikin kwalban, amma yanzu nafasa kuma agm gajiye na ke Aliyu."yakai ƙarshen maganan yana gyara kwanciya, " Okh, mukwana lafiya ni dai wanka zan shiga. " da ga ha ka ya shiga toilet din yin wanka, ko da ya fito ya samu har Umar ya yi barci, nafila ya yi sannan ya kwanta.......... *********** ************ Cikin sauri ta kammala shiryawa sak irin shigan jiya, jeans black and white shirt, breakfast dinma a tsaitsaye yayi tafuce tana gyara gashin kan nata wanda yasha gyara, bread a bakinta tahau motan ta fuce. Isarta station kenan sai ga ASP Zaki ya iso, cikin girmamawa aketa gaisheshi yana amsawa da sakin fuska tare yake da Uncle a office dinta suka zauna ita kuma ta ɗan fita dan ita direct gurin wani taje a can cikin station din dan amso wasu abubuwa,, zaman su na kaman minti 5 sai gata tashigo tana cin biscuits "Sir Zaki good morning" tafurta cikin sakin fuska, ganin abokin aikin nata, ɗago kai yayi ya maida mata murmushin sannan " Madam morning, excuse me" yafaɗa alokaci ɗaya kuma yafuce dan amsa kiran daya shigo mai yanzu, zama tayi akan kujeran ta tana kallon wanda ke zaune yana latsa wayan hannunsa, ganin be ɗago ba yasa itama taɗau file din gabanta tana buɗe wa tare da faɗin " Bisimillah, kar kace na ma rowan biscuit duk da kaɗan ne ya rane a ledan." daɗaɗɗan muryanta yamai amsakuwa a kunnsa tabbas yaji sallamanta kuma ya amsa daganan be sake jin maganan kowa ba sa bo da abin da yake yi a waya ya ɗauke mai hankali. ɗagowa ya yi yana kallonta ita ma anan ta ɗago ta na miƙa mai biscuit din take idanuwan su ta ke idanuwan su suka haɗe, Ita dai kallon shi take yi, ya sanya ƙana nun kaya wando jeans blue sai riga mai dogon hannu Black, gashin kanshi ya sha gyara tsaf sai faman ƙamshi ya ke yi, ga fararen idanuwan sa ma su sheƙi, murmushi ne kwance kan fuskansa. shikuwa ganin kyakkyawan mace choculate colour mai ko ka ce golding skin, kyan sura tana kallonsa da idanuwanta farare ƙal, be san me ya sa ba ya na son irin colour din akin ɗinta, gaba ɗayanta ta burgeshi kuma a karo na farko dayaji wani ya nayi akan wata yarinya. "Amsa ma na akwai daɗi." ya ji ta kuma ce wa sai ya sauke idonsa da ga kallon ta, sauke nauyayyan ajiyan zuciya ya sa ki sannan ya ce "Alhamdulillah" sai ta kai ƙaramin bakinta ta hauci, ya na kallonta ta na karatu ta na cin abin ta kuma ta na ɗan kar kaɗa kanta, kallon ta ya ke yi ko ƙyaf ta ido ba ya yi, ita kam ta na jin wannan idanuwan na sa a kanta, ba ta ɗago ba amma ta ce " Kallan fa?" sai ya sauke idonsa a karo na biyu, wlh tinda yake betaɓa jin mace ta burgeshi ba irin ta, miƙewa tayi ta nufa wani case tadauko document, yanata binta ta kallon yanda take tafiya sai da gaban shi ya faɗin, tana juyowa tanufesa hawa Desk din gabanahi tayi suna facing amma basu mazi juna a, kallon sa tayi tanamai haɗe fuskan bakaman ɗazu ba, bindiga ta janyo aya bayanta ta shaida zuciyar shi ta re da ɗaura bindingan a gurin ta danna har ya to kare da jikinsa sannan ta ce " Kallon ya isa ko in tarwa tsa dai-dai nan." ta faɗa ta na ɗan na bindigan a kan girjin sa sai ya lumshe idanunsa, ya sani a kallo ɗaya ya yaɗa kuma ya ji ta mai "Wlh na faɗa." ya furta kaman me raɗa, murmushi ta sa ki sannan ta koma gunta ta na faɗin "Zan ko tsamo ka." "Ai nashiga ba futa" ya ba ta amsa a dai-dai nan ASP Zaki ya shigo ya na ce wa " Sorry na bar ku." " Da yanzu zan wuce kasan akwai abin zanyi me mahimmanci kaɗauko ni amma ban yi a sara ba tin da na gani, na ji yamin." Uncle yakainan yana kallon Madam ta fahimci abin ya ce dan ha ka tai banza da shi ita tin da ta ke babu wanda ya taɓa kallon kwayan idon ta ya furta ya na sonta sa bo da tanada kwarjini agun maza, Zaki be fahimce shi ba ya zauna ya na kallon aminiyar sa wat o Madam da ke ha ɗa ta kaddunta. " Gasu mun haɗa komai, a tina nina mu bi komai a sannu sa bo da sai mu san takunsa tukun zamu yi amfani da salon sa don kama shi" ta furta ta na mai miƙa mai files ya amsa ya na faɗin " Karki damu Madam meerah, ai tin da aka saki a case din na sanki akwai kwanya, bincike yanzu aka fara." murmushi ta saki ta na ce wa " Hmmm Zaki kenan, yau zolayan ya ta shi kenan." " No gaskiya ce ai Meerah ba ra naje karna ɓa ta ma Uncle lokaci." da ga ha ka ya miƙe shima Uncle ya miƙe da ido tabi su kawai, Zaki na fita sai Uncle ya dawo ya tsaya a gabanta, ba ta ɗago ba amma ta ce " lafiya? akwai abin da ka ke so ne?." " Ina sonki ban taɓa jin yadda naji akan wa ta ba sai ke, bazan wuce ba, ba tare da na fa ɗa miki ba, I Love u. " shi kan shi be san lokacin ya furta hakan ba, ita ko a da ke ta ce " Za ka iya tafiya toh." " I need your digit.". sai da da ta kuma kalleshi sannan tace " Sorry i can't." ta na kaiwa nan ta miƙa ta re da raɓa shi ta fice, ganin ha ka shi ma ya bi bayanta ya na murmushi. END Daga Alƙalamin Pretty Sk. [6/10, 20:30] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ May Allah ﷻ accept all our righteous deeds bring us endless joy, peace, and prosperity. ✨ 🌙 🕋 Eid Mubarak 🕋 🌙 ✨ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK Page 10 *********** ****************** Badikko Kowa aikin gabansa kawai yake yi, cikin sauri-sauri ta gama wanke-wanken sanan ta yi shara, dan yau za'a kawo lefen Radiya gobe kuma na Rabi'atu, abu kaman wasa yau gidan lafiya lau, aiko misalin ƙarfe biyu ƴan kawo lefan suka kawo, har set uku masu ɗauke da kaya dai-dai wadeta irin na masu ɗan hali, don wani malamin makaranta ne za ta aura yana samu dai-dai wadai da, bayan sun wuce suka bubbuɗe kayan kwanin sha'awa. har maƙota suka fara leƙowa. " Gaskiya kayan sun yi kyau Radiya, na ɗauki powder." Ramlat ta furta ta na nu na Eman powder, "ɗauka bara ma na duba miki wasu." zaɓan wasu ɗan abubuwan kwalliya ta yi ta bata, ko banza yau dai duniyan ta yi mata daɗi sosai, dan ha ka ta yini cikin walwala. Mama dai ido kawai ta sa mata ba ta ce ƙalaba. ************************ Rhyeno Estate Da yake yau sunday babu makaranta, abin da sun manta rabon da suyi shine wanke-wanke da shara amma yau sune suka hau aiki sosai dan Babban yaya, tin Asuba ya zauna a Main parlour ya na azkar, sun sha aiki kaman me koda suka gama a Parlourn su ka zauna suna karatu, Allah yaso su ya mai da musu wayoyin, da ma da biyu ya amsa so ya ke ya yi bincike cikin wayan duk da ya na bin komai na su amma basu sa ni ba, sallaman su ya yi amma ya ce Hasty ta tsaya hakan ya sa hantar cikin ta kaɗawa, tasan dole ya yi mata magana duk da yau wata uku kenan da faruwan lamarin. "ko da wa sa idan na ƙara samun labari irin wannan zakiga ne kuranki, wuce ki kiramin Karima." da rawar jiki tabar gun ta na shiga ta kira Karis wacce ita ma tasan dole a ne me ta, ita ta na zuwa warning ya yi mata ya sallame ta sai suka fara gaisawa da Zaki wanda lokacin suka shigo shi da Uncle. ta na shiga Kandy ta ce "Ke me kika yi" Sai da ta sha ruwa ta zauna sanann ta ce " Hmmmm wani teacher ne a school din mu ya ke bibiya ta, ga shi be da ɗa'a ko kaɗan, da ya ke ba section din mu ya ke ba to ni ban sani ba ya kan zo class din mu muyi hira kaman wasa ashe sona yake yi to ni kuskuren da nayi shine ranan na je staff room dinsa, wlh abu na je amsa sai malamin nan ya yi ƙoƙarin ta ɓani shine mukai faɗa na fita, koda washegari na je school a ƙasar Desk di na na ga paper ko da na buɗe sai naga an rubuta 'first and last warning from Baban yaya.' kuma har da sign din shi, ni ko ƙara kula shi banyi ba, jikina ya bani shima an yimai warning dan in ya ganni can za hanya ya ke." shuru suka yi suna mamakin yadda komai Babban yaya ya na an kara kuma ya na bibiyan su, duk da ba ya ƙasar abin na ba su matuƙar mamaki, Hasty jan nunfashi ta yi dan tinawa da nata ''''Sabon page ta buɗe a Instagram ta yita daura videos din ta har da sauraiyin ta wani Nasir, to ranan da ga school suka je party sun sha rawa kuma duk ta ɗaura, aran Babban yaya yakira ta da daddare ya mata kashedi sannan da umarnin ta goge komai kafin ya iso, aikam ta goge dukka'"'. "Hmmm gaskiya duk wacce ta aura Baban yaya ta shiga uku." cewan Beasty ta na cire hijab dinta sai Butter ta ce " Hmmmmmm Allah dai ya kyauta, ni fatana gobe ya wuce kawai....." " Bakiji Pazar M ya ce ba bu in fa ze kuma zuwa ba." Kandy ta katse ta "Da mun kaɗe kuwa." da ga haka su ka can za hira amma kowanne su ya na mamakin Babban yaya kaman wani Aljani, kuma sun yadda ya na ji dasu dan sai kana son abu ka ke ba shi kulawa. Bayan sunyi breakfast Pazars suka zauna a Parlourn baƙi sai Uncle, Shuraim, Pazar R yafara magana cikin sanyi-sanyi kaman Pazar Q dan ha ka yanayin shi yake " Shuraim da ga yanzu ba zaka ƙara barin ƙasan nan ba ba tare da kwarkwaran dalili ba, sannan ina son kasani badan Allah yaɗora ma nakasa ba, da kai ne Abdulmajeed ze zaɓe, saboda ka can canta dari bisa dari, dole yanzu kai Haidar za mu daura a hanya." yanuna Uncle, sai da girjin Uncle ya buga sai Pazar M ya ce "Acikin jam'iyar mu ne ake ta samun rashin jituwa sa bo da za ɓe ya kusa nan da 3mounth ha ka, Aliyu dole kai zan kaiwa jam'iyar domin tsayawa ta karan Gomnan Kaduna." dam gabansa ya kuma faɗin har ze yi magana sai yafasa saka makon hannun da Pazar Q yaɗa ga mai, sai Shuraim ya yi magana ya najin wani nishaɗi a ransa " Gaskiya kunyi zaɓi dan ƙanina yasan komai dan ga ne da harkan siyasa, gashi yasan dubarun mulkin U.S kunga ze gyara mana Nigeria, kuma be da damuwa sanna...." Pazar M ya katse Shuraim cikin ɗan hassala " Ai mun sani ko da lafiyar ka lau ba zaka yi yadda mu ke so ba, ka na da taurine kai, Shuraim a tinaninka kai gyaleka za mu yi a haka ba wani aiki a hannu, kai ne a nan yau kai ne acan gobe, ai ya ishemu a ha ka kai da bindika za mu ne mo muku aiki ban yadda da wani online business din nan ba." murmushi ya saki ɗan jin an kira Adam da bindi. " Kuma nan da wata 3 nake so dukkan ku kuyi aure inbma ku kawo wacce kuke so ko kuma munemo muku." cewan Pazar R sai a lokacin Uncle ya samu damar magana " Banƙi ta ku ba, 27yrs na ke how zan iya mulkin jahar Kaduna Pazars, kun sani ina aiki a office din prime minister na U.S, da gobe zan koma dan akwai ni aiki sosai, Pls pazars ku duba ko a ha ka Babban yaya ze yi, ya fini cancanta ta kowani fanni......." Pazar B ya katse shi da ce wa "Ai mun ga ma magana ka na da 2-3 mounth kafin kafara aiki, ko katura a ɗauko maka dukka abubuwa ka ko kuma kabar shi amma kai da zuwa United States sai kahau mulki, maganan aure ne a farko dan dole ku yi aure kafin lokacin." " Aure ni banda budurwa kuma banson yi yanzu, dan babu me auran gurgu, idan lokaci ya yi zan ne mi wata masakan, na barku lafiya." ya kai nan ya na reverse da keken sa ya fice da idanu su ka bishi har ya fita sai Pazar Q ne ya ce " Share wan can, Aliyu kai fa ka na da budurwa ne?." yana jin ha ka sai ya tina Meerah sai kawai ya sa ki murmushin ƙarfin hali ya na ce wa " Eh Pazar akwai wacce nake so amma bamu gama daidaita wa ba." " Mun ba ka 3weeks sannan wannan maganan ya zama secret domin ga ba ɗaya jam'iyyar zamu girgiza." kai ya ɗaga kawai ya fita ya barsu dan za su tattauna ne, part din sa ya nufa sai dai kan ya shiga yaji muryan Shuraim ya kiran shi, juyawa ya yi ya nufesa, ya sauka a wheelchair din ya hau kan kujera ya na zuwa shima yahau sai da ya ɗaura kansa a kan cinyan Shuraim ya na sauke ajiyan zuciya, Shuraim kuwa gashin kan Uncle yake shafawa a hankali alaman rarrashi, har ze yi magana sai Shuraim ya sa mai yatsa a kan bankin dan haka ya yi shuru kawai sai shi Shuraim din ya kai bakinsa kan kunnunsa ya raɗa mai " ina ta re da kai duk runtsi duk wiya, karka saɓa musu umarni ka ji ƙanina." kai kawai ya ɗaga mai. END Daga alƙamin pretty SK. Ina fatan kowa yayi babban sallah lafiya. Allah ya maimaita mana. Ameen. [6/11, 07:41] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ May Allah ﷻ accept all our righteous deeds bring us endless joy, peace, and prosperity. ✨ 🌙 🕋 Eid Mubarak 🕋 🌙 ✨ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ Page 11 ********* ************** RHYENO ESTATE A tabayan gidansu gurin shuke-shuke wato Garden suke zaune, ranta a haɗe ta ke magana dan ko gaisawa basu yi ba ta zauna dan kiranta ya yi a waya ya ce tazo gurin ta same shi " Wani kalan soyayya muke yi Yaa Adamsi? 2yrs ban ganka ba sannan baka kirana ko chat sai ta facebook muke yaɗuwa, shima sai kayi one month ba ka hau ba, dana yi ma magana sai ka wani ce Babban yaya baya barinka, ba lokaci, how zamu ci gaba da rayuwa a haka, na gaji gaskiya na gaji, rabuwa zamu yi sa bo da kai ba na kula kowa sam amma ban samun kulawa agurinka, Why?." ta na kaiwa nan ta miƙe tsaye sai Adam shima ya miƙe yasan be kyauta mata ba, domin haka ya ke mata to ya ze yi baze iya saɓa umarnin Shuraim ba, amma kafin subar nan ko ma menene ze samu ayi maganar auran na su. " I'm sorry My Sweet kandy, Insha Allah da ga yanzu zan kasance da ke koda yaushe, kuma zan gyara, ai yanzu muna nan ba'inda zan ƙara tafiya na barki, sai kiyi saving number da ma kira ki dan sabon sim ɗi na ne." " ni nagaji da savings numbers din ka, da munyi waya yau to ban kuma samu ka da wannan number. " " Ki ya ƙuri mana Insha Allah komai ya huce kuma jira na ke ki kammala karatu sai muyi aure." " Uhmmmnmmn." Zama ta yi a in da ta tashi, haka shima ya yi ya zauna, zan can hira na ƙorafi suka bari zuwa na soyayya da kewan juna, Khadijah sam ba ta fushi da Adam domin ta na son shi sosai shima haka ya na son ta. Tin lokacin ta na yarin ya idan ya zo gidan suke hira sama-sama tin a lokacin ya ke furta ma ta yana sonta sai dai kawai ta yi dariya, har ta kai lokacin da ta fara son shi, kowa na gidan sun sani amma babu wanda ya shiga harkan su, harta Babban yaya ya sani sai dai ya sa musu ido kawai. A Parlourn kuwa sai da suka dau mintina a ha ka sai Shuraim ya ce "Kawai ka kira su haɗa ma ka komai gobe Adam sai yaje ya amso maka." da kai ya amsa sanan shuraim ya ci gaba da magana " Ka na da budurwa ne?." ya kuma ɗaga kai, "Wow ƙanina hakan ya yi, to yaushe za ka nunamin ita?" Sai a lokacin Uncle ya buɗe baki ya bashi labarin haɗuwar su da Meera, a fili Shuraim ya ke nuna farin cikinsa, da bashi shawaran daya je gidan su dan ƙara tabbatar mata da ya na sonta. ************ ************** KINKINAU Muwaɗɗa Malik shine littafin da suke karantawa a masallacin, sati da lahadi ne kawai karatun, 9:30pm su ka kammala dan awa ɗaya da rabi suke yi. yanzu ma sun kammala kenan sai suka yi addu'a tare da salatin Annabi sannan kowa ta wuce, sai Ustaz kaɗai dan yana son yagama haɗa ta kadun sai ya futya, yana gamawa ya fito yakulle masjid din da mamaki yake kallon Alhaji Abdulqadir da ke jikin motansa, ƙara sa wa ya yi ya na ce wa " Alhaji lafiya kuwa baka tafi ba, ga dare na yi fatan lafiya." ."Malam Ustaz motar ce taƙi tashi nayi-nayi, yanzu na kira driver da mechanic zasu zo." " To ko zamu shiga ciki kafin su izo ne ?." " Karka damu Mal.Ustaz zan shiga cikin mota na zau......" " A'a gaskiya ba ra nayi maka iso kawai, dan ma mota ta ta na gareji ana dubamin da na kaika da kaina." bajira ya faɗi komai ba ya shige gida, murmushi Pazar Q ya yi dan yanajin daɗin karatun malamin nan, cikin ɗan lokaci ya mai iso, aikuwa suka shiga har Parlour suka zauna, Umma ta fito suka gaisa, Ramlat wacce ke Kitchen da niyyan ɗiban abinci dan yau barci ne ya ɗauka akan prayer-mat bayan tabsha maganin ciwon kai dan da shii ta dawo, Umma ta shigo Kitchen din ta na ce wa " Abbuu ya yi baƙo ki haɗo mai abinci kikai mai, ni zan shiga ciki." da kai ta amsa mata sannan ta ajiye na ta ta shiga haɗa musu, bayan ta kammala ta daidaita hijab dinta ta kai musu, hira suke yi akan littan da aka kammala last week Umdatul-ahkam. Gaishesu ta yi suka amsa sai ta ajiye musu komai data ɗauko sai Abbu sa ta kira sauran matan suzo su gaida shi, dan Alhaji Abdulqadir Musa ƙanƙara akwai mutumci, cikin ɗan lokaci su ka shigo dukan su, gaisheshi suka yi cikin ladabi ya amsa ya na mai jin daɗin a ransa sannan ya ce " Masha Allah Malam Ustaz, wacce za'a bani aciki ." dukkansu suka yi dariya sai Abbuu ya ce " Ai su ukun nan an riga ka sai dai naba ka waccan." yanuna Ramlat ya na murmushi, ita ma murmushi ta yi ta ce " To Baba sai da safe." a tare suka tashi suka wuce amma su na jin ya na ce wa " Wai Baba ta ce min ta na ganina ɗan saurayi me jini a jiki." dariya suka yi ta yi har suka shiga ɗaki, suma Abuu hira suka ɗan yi sannan yaci abincin kaɗan ya na kammalawa aka kira da cewan sun iso,, aikuwa suka yi sallama ya wuce, har sai da ya hau mota tunkun Abbu ya kulle gidan. yana jin daɗi dan tina maganarsu ta ƙarshe da ya ce mai " mubar wasa ba tada miji kace?." " Eh Alhaji, su uku ne zamu aurar nanda lokaci kaɗan." " In babu damuwa ina neman ma Babban yaro na ita, sai dai shi masaki ne ƙafarsa ɗaya ba lafiya tin wa ni faɗi daya taɓa yi shekarun baya." " Allah sarki, ai dukkan mu muta ne kuma ba'a gama mana halitta ba, bamu san yadda Allah ze mai da mu ba nan gaba, kowa yasan ku kuna da mutumci w aye zeƙi haɗa jini daku." " A'a kadai fara jin ta yarinyar ta wa kaji zuwa ko next week sai muyi maganan akai idan na zo Saturday, ka ga sai ka haɗa su gaba ɗaya tin da nan da 2 mounth ka ce." da haka suka bar maganan, ko da ya shiga ɗaki sai da ya labarta ma Umma ita fatan alkairi ta yi amma tanajin ba daɗi wai masaki ne, zata so itama ta auri lafiyayyen mutum kaman ƴan uwanta. ************ ************** RHYENO ESTATE yana isa gida part dinsa ya wuce, dare ya yi dan har Aunty ta yi barci ma, shima wanka ya yi ya kwanta. Acan ɓangaren Shuraim kuwa ya na kwance akan bed ya rufe idonsa abubuwa da yawa ya ke tinawa, a haka har Adam ya shigo, zama ya yi sannan ya fara magana "Boss everythings is ready." sai Shuraim ya buɗe idanuwansa a hankali, sai ya kalli Adamsi ido cikin ido yana wani murmushin da ni kai na bansan fassaran ta ba sai ya ce " Okh, wato kai ɗan soyayya kabarni ka je can kai da khadija, wai na yarinyar nan har ta san wani love?." " Meka mai da Sweet-kandyta ......" ya katse maganan dan jin Pillow a fuskan sa. *** "Assalamu alaikum." abinda yafaɗa kenan sai yayi shuru, kusan 2mnt suka ɗauka ahaka sai sautin muryanta mai daɗin gaske yashiga kwanyarsa. " Wa'alaikumul salam, meke tafe dakai " tafurta tana shafa lotions ajikinta dan tin tana wanka taji wayanta nata Ringing tana fitowa ta duba amma ganin number kuma True-caller tasa Aliyu Haidar tasan shine sai da yakira sau biyar ana shida ta ɗaga, " Bansan me zance ba amma wlh naji makamu sosai, in badamuwa kimin ƙawataccan gidan ku gobe zanzo muyi magana dan da gaske nake" " wanda yabaka number dinnan tsaf ze kawoka gidan mu, amma banda lokaci hira gaskiya yanzu kafaɗa abinda ke bakin ka kawai" " I love U, kuma auranki nakeson yi " " When " saida zuciyarshi ta tsaya na wani lokaci dan jin abinda tace, har number yaƙara dubawa itace dai, saida yaseta kansa sannan yace " Nanda wata biyu indai yamiki" " Hmmmm yayi kazo ka nemi izini, amma bansan soyayya ban iyaba kaima na amince ma ne dan naji har raina na aminta, bansan damu da kira aƙalla duk bayan 2dys waya sau 1 yayi kuma zan baka time dan bakoda yaushe nake son kira ba." " Na shiga uku, wlh Beauty bazan iyaba gaskiya " " Not beauty I'm Meerah or Ramlat " " Ohhh sorry Madam " " Goodnight " kafin yace komai tatse kiran, dariya Zaki yasa wanda yake gedan Haidar yana cewa " Wlh Aliyu kayi sa'a kasan Ramlah kuwa, ta tsani soyayya kuma batayi, a Abuja tayi karatu dani acan muka haɗu, ni kaɗai take abota, a duk lokacin da namiji yace yana sonta to sai anyi da gaske inba haka ba sai tace zasuyi faɗa, wani rana har dambe takeyi da wasu dayake macece me kamar maza akwai ƙarfi da brain, ga tsiwa." " Kace nakwaso ma kaina" " aikuwa amma akwai riƙo da addini sosai ga bin gaskiya " a haka sukaita hira abinsu har sukai barci. Bayan wata ɗaya abubuwa dayawa sun faru daga ciki akwai sa ranan auran Uncle Aliyu da Meera, bayan iyayenshi sun je har gidan su kuma yayyan ninta sun bashi dan mahaifinta ya rasu, hakama gurin su Ustaz sunata shirin dan duka su huɗun zai auran, dan tin washe garin ranan yasami Ramlah da maganan aiko batai musuba ta amince dukda kuwa ance mata baya iya tafiya. Zaune take tana waya da Zaki akan case din dasuke dan jiya aka ƙara sakin wani kisan gilla da RASH yayi, hankalinta ya tashi sosai domin Babban jami'in Police aka kashe " RASH mutum saikace aljani bamusan harin saba bamusan farmakin saba, ba sheda baya anfani da kowani abu gurin sharing Videos dinsa kawai datsan gidan Televisions yakeyi, taya zamu kamashi? " " Karki ɗaga hankalin ki nanda 1 weeks zan shigo Kaduna bikin ki, zamu tattauna kuma ya kamata kidau hutu domin kiyi dilka kinsa...." Ƙet ta kashe wayan, batasan tunawa da maganan zatayi aure ji take kaman tace ta fasa amma tinda ƙannan mahaifinta sunshiga maganar tafasa, rufe Idonta tayi tana tina kwata-kwata sau 6 suka taɓa waya da shi koya kira bata ɗauka abubuwa sunyi mata yawa, amma kullum safe, rana da dare sai ta ga saƙon sa na soyayya tin bata karantawa har tafara a yanzu ita da kanta ma take duba wayan nata ko zata ga yaturo, agogo ta kalla ganin 3:15pm yasa ta dau wayanta tashiga contact, number shi wanda ko saving batayi ba amma tahaddace ta, Kira tayi amma harta katse ba'a ɗaga ba tsaki taja har zata aje wayan sai ga kiranshi, tanson ɗagawa amma dole tajira sai da yakusa katsewa tayi accepting takai kunne, muryansa taji ya yi mata amsakuwa, sai tasamu kanta da lumshe idanu gaskiya tayi kewanka sosai. " Madam yau kece kika kurani, Wow naji daɗi Alhamdulillah faɗamin mekike so ko nazo ki gan nine?" " Ba komai yanzu haka uku tayi tini " sai tayi shuru annan taci gaba da cewa "banga ni bane" jitai haushin kanta yakamata sai ta katse wayan takifa kanta a kan Desk cikin 2mnt SMS yashigo, cikin sauti ta buɗe tana karantawa, ta kara ta yafi sau 10, tanata jujjuya wayarta ƙiran hot 11, tana sakin murmushin dabatasan dalilinyin saba, saƙon yafara kaman haka (Imandhayaty - pillar of my heart, a gaskiya kinsani cikin farin ciki mara misaltuwa, ashe kindamu dani nagode sosai, kikulamin da kanki zuwa dare zankira ki Please ki ɗauka, busy nashiga yau shiyasa ban turo ba). aje wayan tayi tanajin daɗi a ranta, take kuma Idanuwata su kai kan rubutun dake facing dinta wanda akasa RASH, annurin fuskarta ya ɗauke sannan ta na tambayan kanta 'waye kai ? yaushe zaka bayya? kuma a ina ? Ina nan ina jiranka............ END Daga Alƙalamin Sk . [6/12, 12:43] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ May Allah ﷻ accept all our righteous deeds bring us endless joy, peace, and prosperity. ✨ 🌙 🕋 Eid Mubarak 🕋 🌙 ✨ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ Page 12 *********** ************** KINKINAU Bayan wani lokaci Su huɗun suke zaune a Parlourn Umma suna kallon wani series me daɗi na korea, sallama sukaji ana yi tare da knocking get din, Zainab da ke zaune a kujeran dake kusa da ƙofa ta fita ta na amsa sallaman, sai ga ta ta shigo ta na faɗin " Ramlat, sahibaty ce ta zo kingant.." ai kafin ta ƙasar har Ramlat ta fita da sauri, a tsakiyar cikin gidan suka haɗu sai suka rungume juna ita da ƙawarta, sannan suka shiga Parlour gaisawa suka yi da Maryam, Hajara cikin sakin fuskan sannan suka koma ɗakinsu, bayan ta ɗauko mata ruwa mai sanyi da zoɓo ta yi mata godiya ta na ce wa " Mama bata nan ne?." " Eh namesake, gaskiya na ji daɗin zuwan ki, Maman Rabi ta barki kenan?. " " Kedai bari yanzu shiri muke yi sosai balle da su Radiya suka yi aure, anko na zo siya karya ƙare, ace Sahibaty ba ta yi ankon ba ai babu daɗi ba." " Ai in ba ki yi anko ba babu magana kinsan kece kaɗai ƙawata, sai dai class mate kawai shiyasa ni bandamu da ankon ba, ban zuwa shagali kowa nasan babu me zuwa na wa gashi saura sati biyu." " Hmmmm haka ne ai, ni ko anko bangani ba, na manta na tambaye ki lokacin da kika zo gidan mu ko colour din na gani." ta faɗa ta na kai zoɓon bakinta " Hmmmmmm ya yi kyau gaskiya, zan nu na miki anjima." " Tom, yanzu dai tin da ni ce babban ƙawa yakamata nasan ango tun kafin biki takwara" " Hmmmm ni kai na ban san shi ba Ramlat." " Kamarya Ramlat? Badai har yanzu be zo ba?." " Eh takwara Abbu ya ce min bayanan ne, sai ana gobe biki ze dawo kinga." " To amma ku na waya?." " Har yau be kirani ba gaskiya, Uhmmm be damu bane share kawai." daga nan suka sauya hira da abubuwan da zasu na biki, ita ma Ramlat badikko ta ba ta labarin yadda suka shirya da Maman Rabi, dariya suka dinga yi. sai misalin biyar na yamma 5pm ta shirya ta amsa ankon amma Ramlat Kinkinau sam taƙi amsan kuɗin ankon, a haka suka rabu cikin ƙaunar juna da cewan in tazo biki kwana biyu zata yi tako amsa mata. Hijab Ramlat ta cire tanajin tausayin ƙawarta domin ta sha wahalan rayuwa a baya amma yanzu ta ga ta canza ta yi fresh abin ta, da yake tana da kyau sai yanzu kyawun na ta keta ƙara bayyana. ******** ********* ******* Rana ba ta ƙarya sai dai uwar ɗiya taji kunya, babban masallacin juma'a USMAN BIN AFFAN MASJEED KINKINAU. misalin biyu bayan an idar da sallan Jumma'a wanda muta ne sun cika maƙil kamar kowacce Jumma'a dan bautan Allah, 2:00pm dai-dai aka aura auran muta ne sama 20 wanda aciki na jiyo an ambaci Muhammad Bashir da Hajara Abdullahi Saleh Ustaz, Muhin Sunusi da Zainab Anas Saleh, Usman Usman da Maryam Abdullahi Saleh Ustaz sai Aliyu Haidar Abdulqadir da Ramlah Musa wato Meera bi sa sadakin dubu dari biyar adalan ba ajalanba. Kabbara aka kuma yi sai kuma can naji an kuma cewa, sai Shuraim Abdulqadir da Ramlat Abdullahi Saleh Ustaz, aure ya ɗauru an gama ɗauran yau, nan ma sai kabbara ke ta tashi da ga ta ko ina, kowa a gurin fuskarsa a sake yake banda Shuraim da ke kan kekensa ya haɗe rai sosai, ya yi kyau sanye ya ke da sky blue na shadda iri ɗaya da na Aliyu Haidar. Adam da ke gefan sa ya tsugunno sai tin sa ya ma faɗin " Dama har da kai auren?" furzar da iskan bakinsa ya yi sannan ya koma yadda ya ke cikin sakin fuska sai ya ce " Hmmmm ban sani ba amma naji a jikina kan cewa Pazars ba zasu barni haka ba amma mubar maganan sai mun koma gida." ɗaga kai Adamsi kawai ya yi, sai ga Zaki ya ƙaraso cikin walwala, shima manya kaya ne ya sanya wanda suka mai kyau sosai, ya ce " Ango ango iyyeee ai ni banji an ce da kai ba ma sha Allah Babban yayanmu." Shuraim be ce komai sai ya miƙa mai hannu suka gaisa. Alhamdulillah taro ya watse a masallaci bayan an ci an sha an rabar domin an yi wasan kuɗi iya kuɗin. Motoci 6 ne su ka shiga babban gidan su, suna isa muta ne ne cike aciki kowa cikin an kon wani tsadaccen leshi Black and pitch. guɗa kawai ke tashi ango Aliyu sai murmushi yake yi wanda wani annurin ya sauka a fuskan shi, ya yi kyau sosai cikin ɗinkin babban rigan, shida ƴan uwan sune matasa kaman shi, dan shi be da friends duk suna U.S. A cikin gida kuwa, mutane ne sosai ƴan uwa da abokan arziƙi, can ɓangaren ladies kuwa sun sha ɗinki iri ɗaya fitted gown sai na bayanshi wanda zasu sa saboda Boss. Masha Allah sunyi kyau sun sha make-up ga wasu ƙawayensu wasu sunyi ankon wasu kuma kayan nomal one jikinsu, Aunty ce ta shigo ɗakin ita ma cikin ango ɗinkin Buubuu sannan ta sanya hijjab ƙaramin, ta na shiga wasu suka fara gaishesta ta na amsawa sannan ta ce "Kufito a ɗauki hotuna sun dawo." ta ke ƴan matan suka hau guɗa, sannan ta kuma magana "kunsan kuwa har da Babban yaya aka daura ma aure yau kuwa." " Aunty wani babban yaya?." Cewan beauty "Wanda kuka sani Yayanku Shuraim mana. muna sai yanzu muka ji mun daisan harda part ɗinshi aka gyara, sannan ɗazu ta ƙofan baya munga ana ta shiga da kawa." ta na gama faɗin haka ta fita tabarsu duk sun hangame baki, Hasty ce ta yi ƙarfin halin ce wa " Mun shiga uku, Babban yaya, yanzu duk shirin event din dinner yata shi a banza in dai yaje kenan." " Keta event kike yanzu ya yi aure kenan zaman gida dole wayyo allah na." Kandy ta kai nan ta na zama a kan gado, ji take kaman ta yi kuka, a haka suka fita dukkansu suka sha hotuna shi dai Shuraim fuskan nan a haɗe kaman hadari kuma yaƙi tambayan su Pazars akan maganan auran. END Daga alƙalamin pretty SK. [6/12, 12:46] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ If your Mum is alive, may she have a long life to witness your success🤲 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ ᑭᖇᗴTTY ՏK Part 13 ************* ************* K.K GRA Nan ma gida ya cika ana ta shagali, can na hangi Amarya Ramlah (Meerah) cikin farin Less dinkin fitted me tattara ta baya da jela, wa'iyazubullah ɗinkin daram, tsam ta fitar da shape din ta sosai, ba ta yi make-up ba amma fuskanta sai hasken amare take yi, Polisawa ne can gefe guda suna cin abinci mata da maza, gurinsu taje tana musu godiya sannan ta fara tafiya sai ta jiyo muryan Zaki yana mata magana sai ta juya dai-dai nan ya iso gabanta " Amarya bakya lefi kin ga yadda kikayi kyau kuwa, ma sha Allah, yabo da godiya sun tabbata ga mahaliccin wannan halittar." murmushi ta yi sannan ta ce " Ai yanzu na gama neman ka, na sha baka zoba ne ai." sai ga kwalla a Idonta sai ta share da tissue ta ra sa hawayen me take yi tin safiyar yau kawai tana jin babu daɗi. "Haba to ai na zo besty ta, tare da ango mu ke mun zo ganin ki." "Ka ce su shigo cikin Compound." da ga ha ka ya fita sai gashi sun shigo da ango da wasu maza uku. tin da ga ne sa idonsa ya sauka a kan ta, be ta ɓa ganin dogon kaya ba kullum sai riga da wando, sai ya ga ashe manyan kayan suna mata kyau fiye da matsun da take sawa. ƙananan mamanta biyu da yaransu ne kusa da ita a haka dai a kasha hotuna har aka gaji, sai kuma aka basu guri dan suyi magana, za ma suka yi da ga can wani gefen idan babu yalwan muta ne da yake gidan yana da girma sosai. " Please hawayen ya isa ha ka, ki yi haƙuri kinji, Insha Allah wannan shine hawayen ki na ƙarshen sai dai kiyi dan farin ciki." sai da ta share hawayen sannan ta kalle shi ta ce " Kayi kyau sosai fiye da kullum." " Ai kinfi Madam, a yau ma na ƙara tabbata da kyawun da Allah yamiki." sunan ta hira dai sama-sama sai ga yan biyu Yusuf da Yunus, gaisawa suka yi da ango sannan suka musu fatan alkairi ********* ********** KINKINAU Nan ma sai ma sha Allah biki ya yi biki ga manya-manyan malamai, an ci an sha a gurin walima, amare duk sun sha hijabai har ƙasa, ko wacce mijinta ya zo sun yi hoto amma banda na Ramlat, hakan be yi mata daɗi ba amma ƙawarta ta nuna mata ba komai bane,' hmmmm sai ma sha Allah kawai, sun yi kyau duk Hijjab da suka sanya su hau fatan su, ƴan uwa maƙil gida, ƙofar gida kuwa maza ne babu ma tsaka tsinke, misalin 3:30 Hajara ta shiga mota dan ita Katsina za'a kai ta sun sha kuka a haka aka rabu babu daɗi, can ma mislin 5 a kazo aka ɗauki Maryam Ita dai Zaria ne, can ma a kazo aka ɗauki Zainab wacce ita ba tada nisa da gidan su layi ɗaya ne ya raba. Har da Ramlat aka kaita sannan suka dawo, Kwance take akan cinyar Umma ta nata kuka Umma na ta ba ta haƙuri da nasiha. " Ramlat ki yi haƙuri, da ma ita rayuwar mace haka ya ke, nasan har da ti nawa da Mahaifiyar ki koh?, Ki ya ƙuri wallahi Ramlat tun da na ke da ke banta tsanar ki ba abin da yasa bana sa ke miki sosai sa bo da Ummanki ta raine ki cikin sangarta sosai kuma na lura ke irin ta ce halinku ɗaya na sangarta shi ya sa bana sakin miki fuska sosai wasa-wasa na sa ba da hakan kinsan al'amarin sheɗan, duk da kina yarin ya ta rasu amma halin ya shiga jikin ki sosai, amma Alhamdulillah hakan dana miji sai kikafi sauran ma natsuwa sosai, ki yafemin idan hakan be miki daɗi ba." ta ƙara sa cikin kuka ita ma " Na gode Umma Allah ya saka da Alkairi." abin da ta iya cewa ke nan cikin matsanancin kuka, a haka azo ɗaukan ta dan ita ta zaci babu me zuwa ɗaukan ta, motoci guda 15 ne, 14 Black sai white wacce tafi ko wacce kyau a tsakiya ciki aka sanyata ta nata kuka, sannan ƙawarta Ramlat ta shiga wata ta gaban ta amarya sai wasu ƴan uwansu. Sannan mota tabar unguwan, kowa ya sha mamaki ganin irin motocin amma da an ce musu ai yaron gidan su Alhaji Abdulqadir ƙanƙara ne zasu yadda subar maganan suna mata fatan alkairi, dan ko da aka kawo akwati an sha mamakin domin guda 24 a ka kai mata kowanne cike da uban kaya. Dukkan su biyun kuka suke yi sai can suka yi shuru, Ramlat ta fara magana cikin shashsheƙan kuka " Assalamu alaikum." " Wa'alaikumul salam." da ga haka sukyayi shuru, dan ko ba'a faɗa ba sunsan dukkansu amare ne, a yanzu Meerah a tamfa ce ta sanya brown da milk sai babban gyalen kayan. Direct cikin Estate da ke cikin baban unguwa ta shahararrun muta ne wato Milinium City, aka shiga da su baban ESTATE din wanda ya sha saɓon fenti masu sheƙi, muta ne duk sun watse sai ƴan uwa na ne sa. a tare aka fito dasu aka kaisu Main parlour, ƴan uwa duk aka da bai baye su, da yake ita ma Ramlat ta janyo hijab dinta kanta na ciki, ita ma Meerah kyalan ya rufe fuskan na ta, a naso aga fuskokinsu amma babu hali, a bababn parlourn suka sauka dukkansu, in da ƴan uwan ko wacce suka ba da ammar ƴarsu, can dai a ka ce a kaisu su shirya za'a je dinner lokaci ya kusa, A part din Momcy suka sauka aka barsu su kaɗai bayan an aje musu kayan da zau sanya, shiryawa suka yi sai Ramlat ta ce " Baiwar Allah, ni fa wlh banson zuwa." " Karki damu baza'a daɗe ba kuma ina tare da ai, sannan sunana Ramlah ko ki ce Meerah duk da baiwar Allah din ce." " Laaa ashe takwara ce ni ma Ramlat na ke." " Uhmmm haka ne amma ke Ramlat ni kuma Ramlah kin ga ƙarshe da bambanci duk da ɗaya ne." dariya suka yi sunata ɗan hira har suka gama, ma sha Allah na rasa wacece tafi kyau a cikinsu, dogon riga ɗinkin gown ce, purple colour , ta yi musu matuƙar kyau, idan ka kalli Meerah sai na ce ta fi waccan kyau amma da ka kalla fara alƙabban mata sai dai ka yi hamdala, farar-farar ce haka choculate colour ɗin ma hmmmm. Su na gama shiri suka rufe kansu da kyale kayan sannan suka fita a ka kai su gurin babban gurin taro. Amare suna zaune a in da ya dace haka muta ne ma. sai ango Aliyu Haidar a gefan Meerah, MC yasa kiɗa mai sauƙin sautin "Aure daraja, marta ba ce mai tarin yawa..." ƴan mata sunka fara takawa abin su. Zaki shi ma zaune ya ke a gefe ya na ta kallon program din sai a ka zo gefan shi a dai-dai kunnunsa a ka ce " Please minti biyu, amarya ce ta aikoni." ya ɗago ya kalli me maganan amma har ta yi hanyan waje, kaman ba zai je ba sai kuma ya miƙe ya fita, tsaye ya ga budurwa mai tsayi ta juya mai baya, sai ya nufe sallama ya yi ta juyo da sauri tare da mai da mai sallaman, sannan ta haɗe rai ta rufe Idonta ta fara magana cikin masifa kamar yadda ta sama idan za ta yi rashin mutum ci. " Na lura kai ne abokin wancan angon, kuma ina zaton shima haka ɗayan, in ban da rainin wayo, ƙawata ba ta son ta zo amma muka lalla sheta mu kazo sai shi yaƙi zuwa, bani numbern shi in kira in zazzaga mai rashin mutum ci, ai wannan rainin sense." ta miƙa mai wayar Ramlat din, furzar da iskan bakinsa ya yi sannan ya sauke ajiyan zuciya ya ce "I'm sorry ba ni ne abokin Shuraim ba and bansan ina ya ke ba." " Oho ni ban number shi na kira na ji dalilin ƙin zuwan shi. " " gaskiya be kyauta ba, kuma ban da number shi...." Fuuuuu ta wuce ta ko ma cikin gurin, ji yayi ta burge shi sosai, koma wa ciki ya yi, a gefan amaryan Shuraim ya hangeta, bini-bini sun haɗa ido sai ta dalla mai harara shi kuma sai ya yi murmushi. Ganin Bababn yaya be zo ba yasa ladies su ka raƙashe suka shashe abin su, a haka har aka ta shi misalin 11pm, gida aka mai da su, ɓangaren daban-daban, aka kai Meerah part din farko wanda ya sha uban kuɗi da gyara, ita kaɗai aka bari kowa ya watse bayan an yi mata nasiha sannan an kaita gunsu Pazars suka sanya ma auran albarka, ita ma Ramlat na ta ɓangaren aka kaita wanda komai nasu iri ɗaya ne, ganin irin kukan da take yi akan kar ƙawarta ta wuce ya sa aka kaita ɗakin ladies. Ramlat zaune ta ke tayi jugum dan ta gaji da kukan tayi shiru, har ɗaya na dare angon be shigo ba aiko tayi kwanciyarta cikin linzimin wani kalan miji ta aura, shin a haka zatayi rayuwa da shi, tin kafin ta sanshi taji bata kyaunar sa ko kaɗan, ace sai a card wedding ta ga sunan sa wai Shuraim (Babban yaya). Su kuwa su Haidar bayan abokansa ko in ce ƴan uwansa sun kawo shi suka musu nasiha sannan suka wuce, sallah suka fara yi sannan suka zauna a Parlour suna ɗan hira tare da cin abinci, bayan sun gama suka shiga bed room, ya lura Merah gaba ɗaya a ɗan tsora ce take ga kuma taƙi sakin jikinta dashi dan haka ko hannunta ba riƙe ba a haka sukayi barci abin su....... To Allah ya baku zaman lafiya ameen. End Daga alƙalamin pretty SK. 6/12, 12:46] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ If your Mum is alive, may she have a long life to witness your success🤲 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK Page 14 ********** ********** Kiran sallan farko a kunnanta dan ha ka ta miƙe ta shiga toilet alwala tayi sannan ta fito ta na tinanin ina ne gabas, can sai ta hango prayer-mat wanda ya fuskanci gefe guda kuma a ta sama anvsa wani abu me ɗauke da sunan Allah wanda aka ƙawa tashi, take zuciyarta ta raya mata nan ne gabas aikuwa ta kalla ta gabatar da sallanta ta na idarwa gurin tayi raka'atanul fajr da Subh sai tabhau karatun alkur'ani cikin daddaɗan muryan nata kaman me busan sarewa. Ɓangaren su Aliyu Haidar kuwa yana tashi ya tabsheta sannan ya fice masjeed, wanka tabyi sannan tabyi sallah duk abin ta ba ta wasa da ibada, lissafi ta hau yi yau satin ta ɗaya ba taje aiki ba kuma tasan sai nan da kusan 2weeks again za ta koma, abin da take ji sam ba zata iya ba, yana shigowa ta ɗago fararen idanuwanta ta kalle shi, sai kuma ta ɗauke kanta, da murmushi ya iso in da ta ke ya zauna gefan gadon ta re da ce wa " Madam kin tashi lafiya?." gani yayi ta ɗauke kanta da ga kallon shi, hakan yasa ya ɗago hannunsa yajuyo da kansa ya na kuma magana cikin raɗa-raɗa. "me nayi to daga kaisuwa kuma?." " Karka sa ke cemin Madam ....." "Sorry Meerah." turo baki ta kuma yi sannan ta sanya hannunta wanda suka sha lalle suka ƙawata shi duk da duhun hannun amma ya fito raɗau sosai. " To wanne kike so?." " Uhmmm." ta faɗa ta na miƙewa da idanu ya bita, cire hijab din jikinta tayi ta sagale a anger, riga da wando masu laushi ne ta sanya sai wannan ƙashin amarci ke fita ajikinta me sanyin daɗi, ga wannan gashin na ta daya zubo baya dan ita ba tayin kitso, gaban mudubi ta tsaya tana gyarawa gashin sai kawai taji ya janyota jikinsa, kallon juna suka shiga yi kowa najin ƙaunar ɗan uwan nasa, a hankali ya kai bakinsa cikin nata suka shiga kissing juna cikin rashin kwarewar su, a haka har abu ya kan ka ma. Basu suka na tsuba sai misalin 8am, wanka suka yi a tare sannan suka shirya, sai suka koma Parlour domin breakfast dan tin da zu aka kawo musu, kallon ta yake yi cikin so da ƙauna mara misaltawa, nu na mata wani babban ƙofa ya yi wanda yake a gefe ya ce mata "Ƙofan shiga Main parlour kenan ba sai kin sha zagaye na, kodan idan zaki gai da iyayena ko kina son yin hira nan za ki bi " ɗaga kai ta yi sannan ta marairaice fuska, tai magana cikin shaƙwaɓar ta. "Ni kace min zan koma aiki amma baka faɗamin yaushe ba ne." " Madam ke da amarya ce kibari nan da three weeks sai mu koma tare." "Ni kade na cemin Madam banaso." sai da yayi murmushi sanann ya ce " To Omry, ni fa wanne zaki din ga kirana dan na gaji da kira na da kike yi da kai ko Malam." Sai tin kunnansa ta kai bakin ta sannan ta ce "Farsi." " Awwwnnn omryty thanks, suna mai daɗi." yafaɗa yana shafa gashin kanta. " Kai ba business kake yi ba ai ko next week ka koma kasuwan ka." "Eh, toh ha ka dai na ce amma soon zaki dan aiki na dan yanzu ne ma nake yi na kanje kasuwa ne kawai." da ga haka suka dinga hira kwanin sha'awa. Ramlat ce ta ɗauko abincin ta nufe ƙofar da a ke ce ta shiga, duk ka ƴan matan su ƙi kawowa sa boda wai karsu haɗu da Shuraim. Sallama ta yi har sau biyar ana shida Ramlah amarya ta fito ta na amsawa, ganin ƙawarta ta faɗaɗa murmushi a fuskanta ta na faɗin "Naji daɗin ganinki ƴar uwa." gaisawa suka yi sannan suka zauna a parlour suna ɗan hira sai Ramlat ta ce " Ango na barci hala, Allah ya sa ban ta kura muku ba?." "Hmmmm to ai be zo ba, banga kowa ba ha ka na kwana da tambayoyi da yawa, shin kodai auran dole a ka yi mai." ta ƙare maganan cikin kuka, da ƙar Ramlat ta samu ta rarrasheta sannan ta ce tabar abin kar ta faɗa ma kowa ta yu akwai dalilin ƙin zuwan nasa. ƙara suka ji ana ƙoƙarin buɗe ƙafan ɗaya daga cikin sauran ƙofofin na ɗakin dan ƙofofi kusan 6 ne, sai kuma a ka yi shuru "Kodai a ɗakinsa ya kwanta Ramlat?." " Oho mai ni wallahi na ji ban ma son ganinsa, har ta auran banso dashi." ta faɗa ta na share kwallan Idonta, sai ji sukayi an buɗo ƙofan a fito a kan Wheelchair, da yake ta baya ya fito sai Ramlat ta miƙe da sauri ta fie tana jin Ramlat na faɗin " Ina zakije, ki tsaya mana." ai tuni tabi ƙofar da ta shigo ta fice, direct ɗakin ladies ta shiga, be kamata mijin bestyn ta ya ganta babu hijab sai gyale shi ya sa ta fice da sauri. tana shiga ta tatta Hasty da Baby ne kaɗai a ciki za ma ta yi suna ɗan hira dan sunfi sakin jiki da ita ban da sauran wai su ba zasu kwanta da ƴar talakawa balle ma kandy halinta daban ne akan talakawa sai mai bi mata Fancy. ************* Miƙewa ta yi tanufi part din da ta kwana har ta kusa shiga tajiyo muryansa mai daɗi da taushi yana magana hakan yasa ta tsaya. "Ina son magana da ke " abin da taji kenan, kaman ba zata dawo ba sai kawai ta juyo ta nufi in da ta ga yakai a keken sa. zama ta yi a can gefe a kan carpet bayan ta gyara zaman hijab din ta, cikin haushin sa da rashin sonsa ta furta "Barka da safiya." sai shuru ya biyo baya kaman ba ze ɗago ba sai ya ɗago ya kalli direction din ta karaf suka haɗa idanu, da sauri ta sauke na ta wanda suka cika da hawaye dan ita sam bata da juriya akan komai kuka yake yi " Kinsan ni masaki ne koh?." "Eh." ta furta tare da share hawayen ta, ya so yayi mata faɗa sosai a kan shiga mai rayuwa data yi amma yaji an ce bata da masaniyar wa zata aura kawai an ce an mata miji ne kawai. "So nake muyi rayuwa kaman mata da miji a waje amma a cikin gidan nan kowa ya yi harkan gaban sa." maganan sai da ya dake ta amma ta daure ta ce "Ko zan iya sanin dalili? Shin dole aka maka da ka aure ni ko yaya ne?." Sai yaji ta bashi tausayi amma ya dake ya ce "No akwai dalili banda lafiya ne, ina akan wani tsarin maganine wanda nan da watanni uku zan ga ma sha shiyasa, sannan ni ban san za'amin aure ba sai a jiya kinga ko bazan iya bijirewa ba." "Shikenan." yaji daɗin amince wa da ta yi babu wani tambayan sai yaji ta burgeshi " Me sunan ki ?." "Ramlat." sai kuka ya kwace mata ace wai mijinta ne besan sunan ta ba miƙewa ta yi take fuskanta tabayyana sosai kaman zata ce wani abu sai ta share ta nufi ɗakinta zata shiga kenan taji ya na ce wa " Zo ki dauki abinci." " Na ƙoshi." ta shige tare da rufo ƙofa, da ƙyar ya dafa ya sauka akan keken ya hau kujera tare da lumshe idanuwan sa, amma jin sautin kukan ta yake yi kaɗan-kaɗan, ji yayi baze iya jurewa dan ya tsani kukan mace, a hankali ya janyo basket din abincin tare da hawa keken yanufa ɗakin nata, babu key dan haka ya tura ya shiga tare da sallama. can kan bed ya hange ta ta nada kuka, sai yaji duk babu daɗi, a daddafe ya hau gadon kusa da ita hannu yasa ya gyara mata hijab din kanta sannan ya ce " I'm sorry Ramlat, ki bar kukan ya isheni amsa kici kinji." daƙyar ta tsai da hawayen ta, amsa abincin ta yi ta'aje gefenta sannan ta ɗan matsa ganin yana gab da ita. "Faɗamin me na miki?." ya tambaya yana mai kallon kyakkyawan fuskan ta mai kyau "Ni shikenan haka zanyi rayuwa ace babu ruwan kowa da kowa, ai ba haka addini yace ba." take tafara jawo mai ayoyi akan aure ta na fassara mai, mutawar zaune yayi jin yadda ta ke ta kawo hukunce hukuncen sosai akan aure, sai da yaja dogon nunfashi sannan ya ce " Shikenan zamu zama abokai kenan kafin nasamu cikakken lafiya koh?." "Ni bance ina buƙatar ka ba amma tuna maka na yi, be ka mata naga kana ƙoƙarin hala na taimaka gurin faɗa wa ba, so nake mu taimaka ma juna gurin shiga aljanna. ba damuwa na amince muyi abota." murmushi ya yi, yau dai an samu macce da ta burgeshi a karo na farko, a ransa yana cewa 'ai wannan dole na zauna dake ko dan ilimin ki da sani nishaɗi.' kallon ta kawai yake yi dan ta burgeshi sosai yana kallon yadda ta ke cin yam ball din a cikin ƙaramin bakinta, sauka yayi yahau keken san sannan ya ce " Na gode kin min halacci duk da ance miki ni masaki ne amma kin yadda kin aure ni, Insha Allah zan saka miki da mafificin alkairi, kishirya nan da 1h ƙanaina zasu shigo gaishe mu sannan za muje gaishe da iyayena anjiman." da ido ta bishi har ya fice, jita yi ta raina kanta sosai duk da shi masaki ne amma kyauwunsa ya toshe rashin ƙafarsa, fari ne fat kaman ka taɓa jini ya fito, haka ƙafafunsa kaman na jarirai. murmushin sa me tafiya da imanin mutum ta tuna....... END ✍️✍️✍️ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ [6/13, 22:30] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ If marriage is part of your plans this year, may Ar-Razzaq open beautiful doors for you & bless you with someone who leads You to Jannah 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ page 15 ************ ************** Suna zaune a Parlour aka yi Knocking, permission aka basu suka shigo dukan su, sun sha kyau kaman za su wani bikin, dan yau akwai walima da yamma, jallabiyoyi baƙake suka sanya da vails, simple make-up aka mu su ma sha Allah, gaishe su suka yi, sai suka amsa sannan Aliyu ya shiga ɗaki ya barsu dan amsa call ɗin ya da shigo wayan sa, shuru ya ratsa parlourn na wani lokaci sai Baby ta ce "Aunty Meera wai ke Police ce in ji Uncle?." Meerah murmushin ta yi ta na mai da Idonta gareta dan kallon t.v take yi " Eh kuma ni sam bansan raini, in mutum ya shiga gabana harbe mutum kawai nake yi." tafaɗa ta na haɗe rai dan ganin irin kallon da Kandy, Beasty, Beauty da Karis ke mata yasa ta faɗa haka. " Kwarai kuwa Madam ba ta da sauƙi ko kaɗan, kubita a hankali shine kawai." Aliyu ya faɗa bayan ya iso Parlourn, ko 5mnt ba su ƙaraba suka fice abinbsu, suna fita Aliyu ya yi dariya ya na ce wa "Ai kin min dai-dai, dan halinsu sai haƙuri, Baby, Hasty da Husty sun fi sauƙin kai." " Tsaf zan se ta su kuwa, dan ni ban ɗaukan raini.". ****** Knocking din ma cikin ladabi suka yi dan ba'a wani jami'in sosai, sun jima suna yi kafin Ramlat ta ji sai ta buɗe cikin sakin fuskan ta na musu iso, da ma sunji labarin ta an ce ƴar talakawa ce, dan haka ba dukkan sune suka gaishe ta ba. A kallo ɗaya Ramlat ta ga ne Kandy sai ta basar dan ta haddace fuskan ta sosai, ita ma dan niƙaf ne da ta shaidata, can sai ga shi ya fito, shima gaishe shi suka yi sannan su ka fice dan ba sa son zama inuwa ɗaya da shi. "Lafiyan su na ga sun fice kaman sun ga dodo." "Ai haka su ke kallona kaman wani mugu." " Uhmm faɗi gaskiya dai." sai da ya yi murmushi sanann ya ce " Yanzu ni na miki kama da mugu?." " A'a amma in ka haɗe rai sam ba ka kyen gani, Yaya Shuraim naji wa su sun ce, wasu kuma Babban yaya koh?." "Eh dukka sunan ne, akwai ma su cemin Boss ma." "Uhmmmm Boss kenan, okh ni ma Babban yaya zan ce yafi Shuraim daɗi." ji yayi kaman ita ce ta raɗa mai sunan dan yadda ta furta cikin ba ma ko wani kalma haƙƙinsa. "Kefa matata ce ya ka mata ki zaɓi wani suna daban haka." "Uhmmm toh ba ra na dinga ce ma Zawji, tin da dai Zawjin ne." " Ni kuma zan faɗa miki amma ba yau ba." Daga nan suka sha hira kaman sun san juna har da ba ta labarin aikinsa na Business Online a haka har suka nufa part din Pazars a can suka tadda su Haidar, nasiha a ka musu sosai sannan Pazar Q yaji daɗin ganin su cikin farin ciki dan Ramlat ita ta turoshi duk da keken me tafiya ne da kansa. ** AFTER ELECTION DAY ** Gaba ɗaya Kaduna state kowa yana son jin saka makon zaɓen Governor wanda ya gudana jiya, T.v gaba ɗaya ƙirgan ƙuriƙu a ke ta yi. Bayan sa'a ɗa ya da farawa aka faɗi wanda ya ci wato Aliyu Haidar Ƙanƙara shine governor na Kaduna state ƙarƙashin jam'iyar NPP me alaman fatanya, ta ke murna ya cika wasu, wasu kuwa a nata ƙus-ƙus a gari. Bayan kwana biyu ya yi rantsu tare da fara aiki, an bashi gidan gomnati amma ya ce a nasu gidan ze zanan, harta Meerah ba ta sa ni ba sai a yau da aka nunnuna a duniya da shafukan sa da zumunta, mamaki ne ya cika ta amma haka tabasar har lokacin daya dawo, nan fa ta fara balbale shi da bala'i, haƙuri ya dinga ba ta amma dagyar ta haƙura. *********** ************* sanye ya ke cikin baƙaƙen kaya kamar kullum yakulle fuskan sa da mask wanda ya kewaye face dinsa, miƙewa ya yi tsaye ya fara ta kunsa mai ɗaukan hankali sannan yakalli camera ta re da fara magana cikin kakkausar muryansa. " Nasan kun jiini shuru kwana biyu, na ɓuya to ina nan kuma ina muku albishir da ce wa yau zan sheƙe muta ne uku, babu ɓata lokaci zan fara da wani ɗan Edo state, sai wani babban jami'in soja wanda ya ke aiki a Abuja sai kuma babban ɗan kasuwan nan me sunan Sunusi Yusuf manajan hatsi." yana kai wa nan ya zatar da hukunsa ga muta ne uku, dattijai biyun da bindiga ya harbesu ɗaya kuwa sa bo da tsoro haɗiye zuciya ya yi. take Camera ta tsaya da record sai ya kalli na gefan cameran wanda shima irin kayansa ne jikinsa sannan ya ce "ku mai dasu in da ya dace, sai gobe da safe ƙarfe 10 ku saki video din." da ga ha ka ya juya ya fara wannan tafiyar na sa cikin ƙasaita da jan aji. ************** ************** Cikin sauri ta sanya riga da wando irin wanda ta sa ba sa wa sai dai na yau ta ɗaura after-drees Black a kai kuma ta yafa gyalan, a matuƙar ruɗa ni ta fita ta bi ta main parlour, sama-sama ta gaidasu sannan ta fice ta shiga motar ta direct gidan commission of police ta nufa, ko su ƴan parlourn jikinsu a sanyaye ya ke saboda video din da suka kalla yanzu, ba ga ɗaya gari ya ɗau maganan a ke yi. dan an zaci Rash ya dena kisan ne ashe hutu ya je, yau daya dawo kuma har muta ne uku ya kashe. ta na isa ta tar da uban ƴan sanda a ciki, ciki ta shiga suna sara ma ta, sun dau 30mnt su na magana sannan meeting din ya tashi cikin ɓacin rai ta nufa office din ta, ko da ta zauna akan kujeranta kifa kanta ta yi tana tina maganan shugaban na su "Nan da 24h mu ke son a sa mu ko da makama ɗaya ne na kama Rash, abin ya yi yawa a ce gaba ɗaya jami'an mu a ban za tin da mutum ɗaya rak ya gagara muku." tsaki ta ja a fili ta na imagine yadda idan ta ka ma Rash za ta mai, Za ma za tay i ta feɗe shi sala-sala, ta dinga ɗaye mai fata sannan ta yayyan kashi gida-gida sannan idonsa da wuƙa zata cire hmmmm abubuwan da yawa ta ke misaltawa a ranta. END Daga alƙalamij pretty SK Sakeenat Abdullahi Mrs I (insha Allah) [6/13, 22:30] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ Page 16 *********** ************** Kuka take tayi cikin ƙunan rai da jin zafi a ranta a ce har mutum uku aka kashe wanda by-mistake ta danna video din ash mugun gani za ta yi, ƙarshe dai wayan faɗin ya yi har sai da ta fashe ya ci screen, da sallama ya shigo a bakinsa ganin yadda ta ke kuka ya sa ya ƙara danna gudun Wheelchair din sa ya nufo in da ta ke "Me ke damunki? Waya taɓaki? Meyafaru?." duk ya jero mata tambayoyin amma babu amsa, sai da kukan na ta ya tsaya tukun ta samu ta ɗago fuskanta da ya yi ja, bayan ya cire hannunsa a kan na ta, cikin kuka ta fara magana " Mutane uku duk ka ya kashe fa, meyasa?." sai wani sabon kukan ya kwace mata, sa ku ya yi ya hau kan kujeran da take ya rungumota ya ja shafa bayanta alaman rarrashi, a hankali ta sa mu ta natsu, ya bata haƙuri, be san meyasa ba, baya son ganinta a cikin damuwa, lallaɓata ya yi har barci ya ɗauke a gurin, kallon fuskan ta ya dinga yi gwanin sha'awa. sai misalin 4pm ta farka da mamaki ta ganta akan gadonta, a haka ta tashi ta yi alwala ta na idar da sallan ta fita ta shiga kitchen girki ta yi mai rai da lafiya, sannan ta jera akan daining, wanka tayi sai ta ɗanyi kallo a TV har magrib ya yi, sai lokacin ta ji dawowarsa, part dinsa ya shiga sai 9pm ya fito dan a ɗaki ya yi sallan isha'i din sa bo da kanshi ya na mai ciwo sosai. ko da ya fito zama ya yi shikaɗai ya ci abincin nabsa sannan ya nufi part dinta a dai-dai ƙofan ɗakin na ta su ka haɗu, kowa ya sakarwa ɗan uwansa murmushi, ba su wani daɗe ba amma sun shaƙu sosai kuma sun fara ƙaunar juna, tare suka zauna a Parlour suna kallo sai ya ke ce mata "Zuwa gobe zan fara zuwa aikin dabsu Pazars suka ne man mu, na so subarni da Online business, tin da ina samu sosai, wai a cewan su hutun na wa ya yi yawa dan ha ka zanfara aiki amma gaskiya ba zanyi aikin gommaniti ba kawai zan jira in dai na ci requesting din da nayi shikenan zan fara zuwa aiki a bank kawai." "Allah ya za ɓa abin da yafi zama alkairi." " Ameen, yau na ga kinyi kyau sosai ne, me ya sirrin?." sai da ta yi murmushi sannan ta ce " Ha ka dai ka ke gani." "Haka ne ma Kifaty." satan kallon shi ta yi sai ta yi saurin juya kanta dan sun haɗa ido gu ɗaya "Zawji Pls ina son gobe na je gidan mu da na yayanta sannan na je na ga ƙawata a badikko kaji." ta kai ƙarshe ta na marairai ce mai fuskan ta re da daidaita muryan cikin ɗan shaƙwaba, salon maganar na ta sai yaji wani irin daban haka, dan haka ya yi shuru na wani lokaci sai ya ce " Bayan la'asar in na dawo zamu fita sai na kai ki duka shike...." be ƙara sa ba ta rungumesa cikin murnan, shima abin sai ya bashi dariya, sannan yaƙara raɗa mata a kunne ce wa "Next week za ki fara zuwa school Poly, dan haka in munje ki haɗo takaddunki." kukan jin daɗin ta fashe mai ta na mai godiya a ha ka su ka shanye rabin dare suna soyayya mai tsafta dan zuwa yanzu sunysan su kansu a buƙace suke da juna amma suna sharewa sai dai shi ya kan tuna ma 'ta cewa ya kusa samun lafiya, be san me ya sa ya ke ma ta ƙarya ba ya na son suyi sunna amma ba yanzu ba duk da suna ƙaunar juna, ya na da babban dalili a kan ha ka, da ƙyar su ka rabu ko wa ya huce part din sa sai da ya yi minti 30 ya na jiƙa kansa a ruwa ya san duk ran da by-mistake ya kwana ta re da ita me afkuwa na iya faruwa, shiyasa ya ke taka tsan-tsan. ********** ************ ********* " Omry ki bar damuwa a kan case din nan, gobe zan haɗa babban taro na jami'ai kuma zan sa Zaki ya dawo nan domin ku haɗu ayi binciken cikin sati biyun nan, abin ya yi ya wa sosai mu kanmu ya taɓa mu dole mu san abin yi." ya faɗa ya na zama a gefanta in da ta bi ta haɗe rai kaman an aiko mata saƙon mutuwa, tin da ya shigo ma taƙiyin magana sai faman kumbure-kumbure take yi ko Uniform din ta ki cirewa " Farsi wallahi duk ranar da Rash ya shigo hannuna sai na sheƙe shi da wannan bindigan ko bindiga ai ya sami sauƙin mutuwa, Allah ne me a zaba da huta dan haka da knife zan mai nawa." da ɗora bindigan a saitin kanshi ta na haki, dariya ta so kwace mai sai ya danne ya na cewa " Omry ba shi ne ba ai, yi haƙuri gaba ɗaya hukuma yanzu ta shiga case kinji." ɗaga mai kai ta yi tana aje bindigan, rungumota ya yi ta baya ya shiga fa ra mata kalamai masu ratsa zuciya harta rage fushin na ta. tukun ta miƙe ta yi abin da ya dace, a tare suka yi wanka, sai shirin barci, a ƙirjinsa ta yi barci shi kuma ya nata shafa gashin nan na ta mai laushi da ƙamshi *************** ************ Ƙofa ta buɗe ta shiga ɗakin nasu, tsaki taja mai tsayi wanda duk kan su suka kalle ta, hijab ta cire ta ajiye a kan sofa zama ta yi kusa da Beasty wacce ke waya da saurayi ta wanda sati biyu baya suka haɗu, ɗan masu kuɗi ne ga kyau sosai, ya na sonta sosai amma yana son rayuwan shagala da ya wa, abin da ba ta son kenan tana son ta canza shi kuma ɗan zata more in dai ta aure sa, dan ta cire tuta, katse kiran ta yi ta na ce wa " Baby excuse me." ta na yanke wayan takalli Kandy wacce take ɗan huci ta ce " Sister what happened?." "I think is Uncle Adamsi? Mrs Love ce fa." Faɗi Hasty ta na kashe datan wayanta, sai Karis ta ce " Maybe wani ne, kun san ba ta fushi da shi ai." " Bashi ba ne Aunty ce." "Me Aunty ta yi." faɗin Baby jin an ce Mamanta ce ta taɓo Khadija, ga ba ɗayan su kuma suka natsu suna jinta sai ta ce " Wai aurar damu zata yi nan da wani lokaci kuma za ta faɗama Pazars, wai ai mun haɗe da matan gidan ba'a gane su waye iyayen, kuma wai ai mun da ɗe da yaa Adam kawai karatun za ta tsaida." dariya wasu suka sa, wasu kuma murmushi, sun san Kandy ba ta san aure yanzu ta fiso ta kammala karatun ta tukunna, shiyasa ta su ta zo ɗaya Adam "To ai yaa Adam ya shirya shi be da damuwa." harara Kandy ta dallama Husty, sai Fancy ta caf ke da faɗin "Uhmmm wa ya ga ranan auran Kandy ƴar a halin ƙanƙara akwai buduri." Dariya suka kwashe sai Kandy ta shaƙa aikuwa suka hau gujeguje a ɗakin cikin wasan da suka sa ba, sai da suka gaji kafin nan kowa ya kwanta tana mai da nunfashi. "Da kunyi addu'a dan wlh ba ni kaɗai ta ce ba dukkan mayan nan." Kandy ta faɗa ta na nuna, Beauty,Besty,Hasty, Fancy,da Husty. " Kina ruwa mu na wa muke toh ai sai dai ku uku banda mu koh Hassana" " Dena ɓata miyan bakinki Husty mu muna nan ai" " Kaji wani zan ce, wai har da ni gaskiya Kandy ni ma kin ce wani abu." cewa Fancy ta faɗa ta na miƙewa da ga kwanciyar " Ai gaskiya ce ko Karis." " Haka ne Kandytah, mu na mu shagali koh Baby da butter." " Dama-dama a ce lokacin Boss baya nan, wallahi ni kai na sai na haɗa na wa shagalin na biki dan classmates dina duk zan gayyata muje special hole hmmmm." " Butter mutumin da ya yi aure ina shi ina barin nan." " Haka ne fa balle ma an haɗa shi da me ƙashin tsiya" " Bansan meyasa Pazar Q yamana haka ba, Babban yaya da yake da matsayi sosai, gashi da kyau duk da ya na da na kasa amma dole akwai wa'inda suka son shi kuma ma su dukiya, kalli dai matar Uncle, jami'ace gasu da kuɗi...." Hasty ta katse Fancy da ce wa " Toh me zeyi da kuɗi shi? nifa matar tana burgeni sosai ba ta da damuwa." ta ke Baby ta amshe zancen "Naga dai talauci da arziƙi duk na Allah ne, ku daina izgili babu kyau sa...." " To uwar wa'azi ko na kowa miki speaker ne?." " Karis ai gaskiya na faɗa da ki yadda ko karki yadda ya rage naku." daganan suka bar maganan dukkansu. END Daga alƙalamim Sasakeeee (Pretty Sk) [6/14, 07:13] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ Page 17 ****************** **************** Gari na wayewa ta yi wani miƙa a kan katifarta wanda yanzu ita kaɗai ke kwanci a kai, aiki ta fara yi ta na gamawa ta yii wanka har lokacin Maman Rabi ba ta fito ba, ɗaki ta koma ta ɗauki wayarta ta na karanta Novel me suna DAGA INA TAKE by Pretty sk, a haka ta wuni a kan wayarta ƙiran Tecno A31, kusan wuni ta yi a haka aiki kaɗai ke fito da ita daga ɗaki, basa wani hira yanzu da Maman Rabi kowa harkan gabansa yake yi, ita duk da ta ƙosa Babanta ya samo mata makarantan da za ta koma ko waec ta yi. Misalin 7pm bayan ta idar da sallan magrib ta jiyo sallaman ƙawarta kaman a mafarki, da sassarfa ta nufi compound din aikuwa suka yi kicibis da takwararta cikin nishaɗi suka rungume juna suna mai jin daɗin ganinta, ɗakinsu suka shiga suna hiran yaushe gamo. " Naji daɗin ganinki, shi to ba zai shigo bake nan?. " " Eh ai gidanmu kaɗai ya shiga ya gaida su Abbuu, yanzu wai zaije ya dawo yabani minti 30 kawai." " Allah sarki aiko ya kyauta ki ce har gidan Zainab kika je." " Ai kuwa, ha ba takwara kibar abincin a ƙoshe na ke." harara ta watsa mata ta na ce wa ta re da ci ga ba da zuba abincin " Ai nasan bakya son cikin abin gidan nan, alright karna ba ki guba koh." jin haka sai jikinta ya yi sanyi dama sun saba kullu in ta zo sai ha ka ta faru da su, ci ta yi ba sosai ba dan a ƙoshe take, hira suka sha da ga bi sani ta shiga ta gaida Maman Rabi wace yau zazzaɓi ke dukanta. Lokacin ya na cika ya ko kira ta a sabuwar wayan daya siyo mata jiya da amma ɗazu da safe ya ba ta, sallama suka yi a kan ya ka mata ta zo ta yi mata one week, har bakin motan ta rakata suka gaisa da Shuraim ya amsa cikin walwala. ta na komawa ledan da ta kawo mata ta buɗe dan ganin menene a ciki. Babban leda ne baƙi budewa ta yi nan fa ta fara tozali da abubuwan ci iri-iri madara, sugar, millo, bread, egg, dasu sweet da biscuit sai wani ledan daban, tana buɗewa ta ga tsohon wayarta ne ta re da paper, tabbas ta ga sabuwar wayarta har ta yi mata Allah ya sanya alkairi, paper din ya buɗe ta fars karanta wa tinda da Hausa a kayi rubutun " Sis na gyara wayan sai ki riƙe babu abin da zanyi da shi, ba ta da matsalan komai, kiyi manage please kinsan bana son godiya koh, karki kirani akan wannan ɗan abun. Ina miki fatan alheri sai ki buɗe WhatsApp tin da dama wayanki bata yi kinga kullum muna online zan dinga turo miki data lokaci bayan lokaci." Hawaye ne ya zubo a idanuwanta tasan ƙawarta ta a kwai kyauta dan ko a da ba ta zuwa haka nan. jita yi ta ƙara ƙaunarta fiye da misali, ta san ko ta kirata ba za ta ɗaga ba dan haka ta tattara komai ta kaiwa Maman Rabi ta gani, cikin jin daɗi ta amsa ta a dana, ɗakinta ta koma taci gaba da godema Allah a kan abin da ƙawarta ta yi mata, da yi matan fatan samun rabo nan kusa, da farin ciki a rayuwar auran su. ************* ************** Ta ra da ina za ta sa ka kanta dan murna, satan kallon shi ta yi, waya yake yi kuma hankalin sa nakan System dinsa dan ko ina ya na tare dashi, a dai-dai nan Adam ya shiga Babban get dinsu dan shi ne ya yi driving dinsu. parking lot ya nu fa ya yi parking, sannan ta fita ba ta jira shi ba ta san masjeed se shiga dan an kira Sallan isha'i, aikuwa ta shiga Main parlour dan gaida su Momcy dan zuwa yanzu duk sun sa ba sosai harda Meerah dan ma ita ba ta wani zama saboda aiki. da sallama ta shiga cikin, samu ta yi dukkansu ƴan matan suna hira kwanin sha'awa. Twees da Baby ne kaɗai su ka gaisheta ta amsa ta na za ma a ɗaya daga cikin kujerun parlour, Kandy ta zabura ta miƙe ta na ce wa " Talauci masifa ne, Allah ya shiga tsakanin mu dashi." " Ameen dai." Beasty ta furta ta na taunar chewing gum, in da sabo ta saba da iskancin muta ne biyar dan duk zuwa yanzu duk ta shedasu, ita dai Butter ba ta wani yi mata iskan ci amma ta na team ɗin su, murmushin yaƙe ta yi sannan ta miƙe ta zo dai-dai gaban Kandy ta ce "Hmmmmmm na lura ƙaramin hauka na daminki, dubeni da kyau babu talauci a jikina, idan kuma ni ce bakya so ki ce ma Shuraim din ya sakeni, so what, shi na ke aure ba ke ba, kuma zanyi maganin ku ba ra ya shigo." kowa na wajan shuru ya yi, ba su zaci za ta iya mai da martani ba, Meerah wacce ke fitowa daga Part ɗinta, ta ji abin da Ramlat ta faɗa kuma ta gano in da zance ya ke, tun kafin ta ƙaraso ranta ya ɓaci, buɗa baki ta yi da zafi-zafi ta ce "Khadija hauka kike yi, me kika sha kike faɗa ma matar yayanki baƙaƙen magana." " Ki barta so ta ke ta zubar manna da mutumci to yanzu Pazars za su shigo kuma yau sai a tantan ce." faɗin Aunty wacce ta fito daga kitchen, ta ke suka ji sallama dukkan su Pazars din harda Shuraim, suna isowa Pazar M ya tambayi ba'asin me ke faruwa, take Husty ta fa ra koro bayani har ta dire, wani irin kallo Pazar B da ya yi mata yasa ta ɗan ɗauke nunfashinta na seconni kuma ta dabur ce. "Yayana shin kana sona ko baka sona? duk da ni ɗin ƴar talakawa ce, mara dukiya." Ramlat ta faɗa ta na kallon Shuraim wanda ranshi ya yi matuƙar ɓa ci " Hmmmmm wallahi Kifayaty, ina sonki fiye da tinaninki, ke ma kinsan haka dan ha ka kowa ma ya sheda hakan. Ki yaƙuri da abin da ta miki." har cikin ranta ta ji daɗi dan haka ta kalli Kandy ta ce " To kinji dai ya na son ƴan talakawa a haka, dan haka ki fita a idanuna nasan kin girmeni amma yayarki na ke a yanzu, ina da shuru-shuru amma idan aka kai ni bango banda kyau sam hmmmmm." ta nuna ma ta yatsa alaman warning ta re da sauran mata biyar ɗin, Juyowa ta yi ta gaida su Pazars sannan ta tura keken sa har bakin ƙofansu sai ya buɗe ba ki ya ce "Kubiyo ni yanzu." daram zuciyar Khadija ta buga da sauran dan ita ba tai tsammanin za su shigo a wannan lokacin ba, sun sani yau za ta ci ubanta a kunsa harda su koda babu ruwan su, bayan shi suka bi Pazars Q ya na ce wa " Kwanda ya yi maganinku marasa kunya kaji wani banzan zance, yara dai ta da shirme, Allah ya shirya mana ku." "Ameen, ai ya ga ma su zo na musu nawa.' faɗin Pazars R, ƙara sawa suka yi suka zauna anan ne sauran matan suka fito dan ba suji wani hayaniya ba. Suna shiga parlour din suka ga Shuraim ne kawai ya na zaune, ƙarasawa in da ke suka yi, cikin ladabi suka tsugunna a ƙasa suna facing na shi, ya ma rasa ta ina ze fara hukun ta su dan haka ya kira Ramlat tako fito bayan ta ajiye hijab dinta har tayi alwala. " Yallaɓai gani." " Me ya da ce na musu?." sai da ta saki murmushi sannan ta ce "A musu haƙuri, idan kuma wata tasake ni na ishesu kasan kuwa yadda na iya rigima? Kawai ban san hayani ya ne amma Ramlat na ke fa." " Hmmmmmmm." " Kabarsu amma ka musu warning dan wallahi duk wacce ta kuma min haka sai na ji ma ta ciwo, kuma in nuna mata banbancin talauci da dukiya, Allah na tuba, hausawa suka ce kafini gidan uban na fiki gidan miji, waya sani sai ka ga wata a ciki Allah ya kaita gidan da babu duk da bana muku fata domin ku ƴan uwan na ne." " Maganar haka yanke Shike nan Queen." " Bara na yi sallah zan musu lecture me zafi, suma su ɗauko hijab suyi anan sai na musu wani karatu akan talauci da arziƙi." " An gama, Baby ɗauko muku hijabs" miƙewa ta yi ta fice tanabjin daɗi dan ita Aunty Ramlat na burgeta, bayan ta ɗauko ta dawo ganin babu kowa a parlourn ya sa tanemi ɗakin da suka shiga, can ta shiga wani babban Bedroom, a nan ta sa mu wasu sunyi alwala, ta re suka yi sallan sannan suka zauna Fancy ta na ce wa "Kandy kin janama raini agunta yanzu." " Uhmmm mu kuma mana shuru ha ba, kubarmu muji da ɗaya mana." Husty ta furta sai sukaji sallaman Ramlat sannan ta ce su fito. Kaman kar wasu su motsa amma ha ka suka fito, a parlourn suka zauna dukkansu a ƙasa sannan Ramlat ta fara huɗuba cikin kwarewa, hadisai ta dinga kawo musu masu ratsa zuciya, amma a banza dan su Fancy haushinta suka ƙara ji. "Aunty Ramlat please zan dinga zuwa ɗaukan karatu." " Baby ni ma gaskiya harda ni" cewan Hasty, sannan Husty ita ma ta ce " Gaskiya nima haka." " Karku damu zan sa muku lokaci." take sukaji jiniyan motoci sun fara shigowa gidan nabsu, sunsan Aliyu ne dan zuwa yanzu cikin tsaro suke, saboda jami'an tsaro ta ko ina, sallaman su Ramlat ta yi suka fice. Shigowa ya yi bayan jami'an shi sun mai rakiya har bakin ƙofan nasu, Hajiya da Momcy kawai ya samu dan haka ya gaishesu sannan ya shigw part dinsa, samunta yanyi tana kallo a TV, da sauri ta miƙa ta rungumesa ta na ce wa " Barka da zuwa." " Yauwa ya gidan." "Alhamdulillah." daga haka ta rakashi ya shiga toilet danyin wanka. ****** suna fita Ramlat ta zame ta kwanta akan cinyar Shuraim wanda fitowan shi kenan ya zauna a gefenta. "Zawjin baby cikina yamin zafi." ya najin daɗin sunan nan, cikin na ta ya kalla wanda yabke cikin hijab a shafe ya ce "Meyasa ba ki faɗamin ɗa zu ba har muka dawo gida sai kitashi muje asibiti koh." "A'a ba sai munje ba ze dena." ta faɗa Idonta a rufe sai ɗan hawaye yake gangarowa. sharewa ya yi da yatsan shi ya ce "Kamar ya ba sai munje ba ko kin zama doctor ne?." " Uhmmmmm ze dena kawai." " How ko p.d ne. " "No, abu ne nasha ɗazu....." sai ta yi shuru "Me kenan kuma a ina?." gyara kwanciyar ta yi ta na canza hiran "Baby me ya sa mi ƙafarka ne naji an ce lafiya aka haifeka kuma kaman shekarun ba ya ne hakan ya same ka." "Uhmm Kifaty, Wata rana ne naje SIDI AND SONs Ina tafiya akan step ashe an yadda banana shell aikuwa na ta ka shine na zame na faɗo, kinsan ko ina tiles ne na bugu sosai dan tin daga saman haka na faɗin har ƙasa, Direct sai asibiti da ƙyar na farfaɗo, sai dai me anyi-anyi ƙafar ta hagu ta motsa amma ina, sam babu sa'a abu kaman wasa sai nakasa tafiya., naje country's dayawa amma babu sa'a at the end na haƙura kawai." jikinta sai taji ya mutu sosai, a hankali ta ce " Ina mai baka haƙuri kaji, Allah yasa ya warke." wayan shine yaɗau ƙara ganin number dake kira yasa yasaki ɗan murmushi mai sanyi, wayan na katsewa saƙo ya shigo ya ko buɗe ganin me aka turo yasa farin cikinsa ya ƙara faɗaɗa, juyowa ta yi takallesa ta ce " Baby wannan murmushin fa ?." "Na samu aiki and gobe zanfara zuwa." murmushi ita ta yi tana hamdala, sai kuma ta ruƙo hannusa da ƙarfi jin cikin na ta ya karta, jita yi ya ƙulle sosai hakan yasa ta da burce, ya na ta mata sannu har ya la fa. ya dinga roƙonta suje asibiti ta ƙi, ɗakinta suka je ta kwanta kan bed ta na riƙe da hannunsa sannan ya ce " Me kika sha?." "Da na je gidan Zee ne ta ɓani wani abu kaman tamarin juice aikuwa nasha shinefa kawai." " Juice ne ko mene ?." " Na sha juice ne amma wai maganin ne." " Maganin mene?" Shuru babu amsa sai da ya maimaita mata tukun ta ce " Maganin sanyi ne." " ban yadda ba, ƙarya ba ta miki kyau ina jinki." " Uhmmm uhmmmm wai na matan aure ne fa kawai." ya gano zancan dan haka ya jingina kansa a jikin bed din ya na furzar da iska a bakinsa. " Shikenan ki shirya yau zan biyaki haƙƙinki, ɗaukan alhakin ya isa haka." ya na kaiwa nan ya koma kan kekensa ya fice da ido ta bishi har ya fice, dariya ce ta kwace mata. " Ashe na iya acting, wow a ta famin gaskiya." sai kuma jikinta ya yi sanyi da sauri ta miƙa ta sama ƙofan key ta ma dariya ta kwanta dama ta gaji barci kuwa ya yi gaba da ita. END Daga alƙalamin pretty SK✍️✍️ [6/14, 22:35] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ page 18 ************* ************** Zip ta zuge da ƙyar harda nishi, Wow ma sha Allah da ta kalli kanta a mirrow ɗinkin ya zauna tsam-tsam ya bi ko wani rami, tudu, lungu da kwari ya yi ɗas, ita kanta tasan manyan kaya su na ma ta mahaukacin kyau kawai ba ta son sa wa ne tafi so wando abin ta da riga. flat shoe ta sa ta nufa Parlour, in da yake zaune ta nufa ta na takunnan na ta kaman macen ɗawisu, tin kafin ya kalleta ya san ta haɗu, idanuwansa ya buɗe a hankali ya kalli yadda ta tsaya a gabansa, fuskan babu kwalliya amma ta yi kyau leshi ne ya ƙarbi fatarta, bakinnan na ta turoshi alaman rigima ta keji, matsar da abubuwan gaban shi ya yi ya miƙa mata hannu, kaman ba za ta kama ba sai dai ta kama aiko ya janyota ta faɗo mai ajiki " Ma sha Allah OMRY kin yi kyau sosai." " To ba ra na je na cire koh ai ka gani." " Ai da ga yau ni dai kalan shigan nan nake so kidinga min in kin dawo aiki." " Uhm Farsi a'a gaskiya ni dai damuna suke yi, kuma duk sun matseni sosai." "A haka nake so." tin ɗazu ta ke jin barci amma ya ha nata wai sai ta yi mai kwalliya da manyan kaya, babu shiri ta yi amma ya sha ƙunƙunai kala-kala. "Shi ke nan tinda bakya son abin da nake so jeki cire kawai na gode." " A'a uhmmm uhmmmmm uhmm, zan dinga ma ka ba bu damuwa, I'm sorry." Murmushi ya yi sannan daga ha ka suka sha soyayyansu abin du. ***** ɓangaren Shuraim kuwa ko da ya shiga ɗakinsa, wanka ya yi yana tinanin yadda ze yi da Ramlat, koma wa ya yi jin ƙofan a kulle ya yi murmushi sannan ya koma na sa ɗakin ya kulle da keys guda biyar, ya sa sakata sannan ya kunna haske ɗakin madaidaici, a hankali ya sauke ƙafafunsa akan makeken carpet din da ya maƙale ƙasan ɗakin, cak ya miƙe tsaye da wannan ƙafafun na sa, ya tsaya ba tare da jin gina da komai ba, amma be ta ka ba, ɓalle butura rigansa ya yi, uay aje a gefe mirrow, ta ku ya farayi da ƙafan hagu wacce ita ce me ciwon kallon mudubin ɗakin ya yi ya na kallon irin halittan jikin da Allah ya yi mai jikinsa a murɗe ta ke, gashi da faɗin sosai, sak dai masu ɗaga ƙarfe, ta ku uku ya yi ya ɗauki yawan shi ya latsa number ɗa zu bugu biyu aka ɗauka, cikin kakkausar muryan wanda ɓantaɓa jin ya yi magana da shi ba ya ce "ku tawo yanzu." sannan ya katse kiran, close set ya nufa ya buɗe sai ga uban kayan sa wa, wa'inda suke a gare, hannu ya sa ya janye kayan ta ke bayan close set din ya bayyan cikin dubara ya ke taɓa wasu waje wanda duk in da ya taɓa sauti kaɗan ne ke fita, harufa huɗu kawai yasa sai ga gurin yana rarrabewa biyu, take lungu ya bayyana a ciki aikuwa ya na shiga ƙofan ta kulle, dogon lungun ya bi sai haske walwal suka fara bayyana, cikin minti 3mnt ya isa wani ƙofan wanda hannunsa kawai ya ɗaura ajiki ya yi scanning akuwa ta buɗe ya sa kai ya shiga, be yi mamakin ganin muta ne uku na jiran shi ba, gaishe shi suka yi ya amsa da kai kawai, ama ya yi kan wani kujera wanda yake kallon na su kujerun, "Boss yanzu na sauke video din akan sabon page din dakacye na buɗe, amma aganina hakan be da ce ba saboda za a iya bibiyan mu kuma....." "Adamsi kai ma kasan Oga mayen computer ne so wannan ba matsala bane." cewan na gefan Adam din, sai shi ma ɗayan ya ce "Gaskiya ka faɗa Skiddo munsan Yallaɓai ai." " Haka ne kuma Spider." faɗin Adam, sai suka mai a hankalinsu ga ogan nasu wanda ya ta ɓa kan table din sai wannan maginin Tv nan yabayya, suka mai da hankalin su a kai. " Gobe misalin ƙarfe 9am na safe zaku kawomin shugaban betir na ƙasarnan, koma yayane ni dai 9am ya shigo hannun ku." da kai suka amsa kawai, sanann suka dinga bincike akan abubuwa da yawa, Sai 2am suka kammala ya miƙa tsaye ya na kallonsu sannan ya ce "Za ku iya tafiya 6hs, ya rage muku." da kai suka amsa sannan suka fita ta wani ƙofa wanda ze sa da su da ɗakin Adamsi. gyara zama ya yi ya kunna wani system din ya na kallo ko ina na gidan akwai camera wacce yasa ba tare da sanin kowa ba, baya shiga in da be dace ba dan haka abubuwa ya dinga kallo balle ma akan ƙananan sa, ya na gamasa sai ya duba na Kifaty, can ya hangeta ta na barci sai yaja videon ya koma baya anan ne ya ga duk abin da ta yi bayan ya fita, dariya ya yi ya na ce wa " Wato ƙarya ne hmmmmm zamu haɗu gobe ai." sai kuma ya ɗauki wayansa ya tura sms ya na kallonta ta cikin Camera, saɓon na shigowa wayanta ta duba ta re da kashe wayan da suke yi da saurayin ta, ganin baybban yaya ne ya rubuto SMS yasa ta buɗe da rawar jiki. yana kallon ta yadda ya ga ta daburce sannan ta kwanta, Murmushin ya yi ya na jin daɗin yau ɗin shike nan haƙonsu ta cimma ruwa dan ta wayan ƙawar ta sa ya samo komai da komai saboda saurayinta yaron mutumin da suke hari ne, shuru ya yi sannan ya miƙe ya kashe ko ina ya koma na sa ɗakin ya kwanta ransa pesssss a zahiri amma can ƙasa akwai abubuwa da ya wa sosai wan da Idanu ba sa hange haka ƙwaƙwalwa ba ta lissafawa sannan baki ba ya furtawa. End. Toh fa Alƙalami ya fara zafi sosai, jinjina ga J.A.W. [6/15, 22:28] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ ᑭᖇᗴTTY ՏK✍️✍️ Page 19 ******************* *************** "Hello Boss." jin ba'a ce komai ba ya sa me maganan na cikin wayan ya ci gaba da maganarsa cikin girmamawa "Akwai matsala a yadda na fahimci komai, ƴan jam'iyar suna tsangwaman Aliyu Haidar duk da ya na babban matsayi, gani suke shine ƙarami a ciki dole su juya shi kuma a kan gaskiya ya ke, YAA-RASH, yanzu umarnin ka kaɗai muke jira a kan komai, sannan mun samu nasaran sato Alhaji Mansir." "Ok" abin da ya faɗa kenan ya katse wayarsa ya na kallon Kifaty wacce ke gefansa ta na cin lunch, murmushi ya yi ya na tina duk ranan da Ramlat ta fahimci shine wannan mutum da ya ke girgiza mutanen Nigeria wato RASH dole ta rabu da shi gashi ya na so ya sosai. " Baby yanzu pharmacy zan karanta?, na fi son low fa." " Karki damu za ki iya, kodai mu canza kawai." " Eh gaskiya." "To sai ki canza amma aikin Asibiti na keso kinji." "To." ta faɗa ba dan taso ba kawai, **************** ************** Bayan biyu Ɗaya abubuwa da yawa sun faru ciki har da fara zuwa makarantan Ramlah wacce ke karantan Pharmacy, dan ta ga yafi sauƙi, ta fara zuwa poly abinta in da Shuraim yasa mammata Driver ya dinga kaita da dawowa. Ɓangaren Meerah kuwa suna ta bincike kaman tashin hankali dan RASH yanzu duk bayan sati ɗaya ze saki video na kisan wani. kowa cikin fargaba yake akan wannan mutumin, kuma mafi ya wa an fi kashe muta ne a kaduna, shi yasa jami'an ciki su kafi ya wa sosai, harta Zaki ya dawo Kaduna dan haɗuwa gurin zaƙulo wannan masheƙin amma ko makama ɗaya basu samu, sannan a ɓoye Governor Aliyu Haidar yasa an fara bincike ƙarƙashin ƙasa a kan duk wanda ake kashewa bi sa ɓoyayyen jami'a sa Sunusi, harta su Pazars abin na basu tsoro sosai yadda ake kisa kuma makashin cikin rashin imani yake aikata kisan. Ɓangaren ladies kuwa cikin matuƙar ɗar-ɗar suke da Babban yaya saboda dai-dai da wani abu suka aikata sarai yana jin cikin ƙanƙanin lokaci, shi ya sa dukkansu suka mai da hankali ga karatunsu, sananne time to time yakan shiga ɗakin su ɗan binciken karatun su. Ita ma Ramlat Badikko ta koma wata makaranta Saleem international School in da ta shiga SS 2 ta fara karatun, zuwa yanzu sun fara soyayya da Zaki tun wani zuwa da ta yi gidan ƙawarta suka haɗu ana ne ya samu har suka yi exchanging numbers, cikin ikon Allah suka fara ƙaunar juna da soyayya me tsafta, sannan suna shan chat da aminiyarta dan ko da yaushe suna online sai dai in sunje makaranta, harta Assignment idan Ramlat badikko ta kasa sai Kifayaty ta taimaka mata. ************** ***************** "Wai nikam me yasa Ya Adamsi yake miki haka ne, ya ka mata zuwa yanzu ayi magana koda ya yane, duk da nasan su Pazars suɗin dai su zasu tsaya mai." " Hmmmmm ke dai bari Fancy na rasa me ke damunsa ko tani bayayi ma sai yasamu lokaci, kina gani rabon da muyi waya na manta ya na da waya amma number shi kullum a kashe." Khadija ta rufe idanunta jin zafin abin da Adam yabke mata, Fancy da ke fuskantanta ta sauke ajiyan zuciya ta na ce wa " In sha Allah komai ze yi dai-dai soon, yanzu kawai kibari muhaɗu dashi, kwanda ke Sis kuna son juna, kawai wasu ɗan abubuwa ne ke hana shi, amma ni fa, hmmmm ina matuƙar son Zaki amma yaƙi ba ni fuska, har numbersa na sa mo a wayan Aunty Meerah amma a banza, Infact an cemin ya na da budurwa, hmmmmmmmm." "Haka ne ki bari zuwa an jima idan ya dawo zamu je mu same sa kawai." dajin wannan shawaran suka tsaida cewa zasu je in ya dawo, ilai yana dawowa Karis ta shaida musu da yake a gidan ya sauka amma a ɗakunan waje saɓanin wancan zuwan, sallama suka yi tare da Knowking "Yes coming." abin da aka faɗa kenan, a hankali suka murɗa handle din suka shiga da sallama da kai ya amsa saboda waya yake yi, kallonsu ya yi cikin ƙaunarsu, sunyi kyau sosai, Kandy Black abaya tasan ya fuskan nan fayau babu make-up, ita kuwa Fancy less blue tasan ya ɗinkin riga da skit nomal, ta yi kyau dan har simple make-up ta sa Baby ta yi mata, su kuma kallon Zaki suke yi domin kayan aikinsa ne a jikin sa, sunayi masa matuƙar kyau, gawannan sajen nasa ma sha Allah, a hankalin kunnuwansu suka fara juyi musu abin da ya ke faɗi a cikin wayan "Haba ƙauna ke ma dai kinsan bana so ko." Dam, Daram, zuciyan Fancy ta buga da ƙarfi, kallonsa ta ci gaba dayi ganin irin farin ciki da nishaɗi na mamaye sa, Cikin kullewa ta miƙe ta nufesa, gyalan da ke kafaɗarta har sai da ya faɗin, sam ba ta ji ba ta gani harta Kandy ta tsaida ta amma ina kawai nufansa tayi, hannu ta sa ta fizge wayan tare da cillar dashi kan sopan da ke right side, yariga yasan me ya kawo su, ta ke fuskanta ya haɗe annuri ciki ta ɓace, wannan ainiyin Zakin ya bayya wani tsawa daya sake mata ya sa ta tina wanene ZAKI. mutum ne shi amma mai wiyan sha'ani, cikin rawan murya ta fara magana "Yaya Umar ka san ina son ka, ina ƙauanrka me yasa ka ke kulawa wata banza ƴar iska can......" " Ƙeeeeee." kit ta yi shuru domin cikin ƙara ji da ihu ya yi magana kuma ya na kai hannusa saitin fuskanta amma ya tsaya dan besan ya mareta domin dole sai an kaita asibiti, harta Kandy ta ji tsoro tasan Uncle Umar be da wasa wani lokaci, durƙusawa Fancy ta yi har ƙasa tana mai fashewa da kuka gami da haɗa hannuwa ta fara magana "Zaki wallahi ina sonka, kai ma kasa ni na kamu da soyayyan ka dan Allah ka tausaya min." jiyayi jikinsa ya yi sanyi amma be mu na a fuska ba ya ce "Wato tsabar rashin kunya yau sai ki ka biyoni ɗakina kenan, kin faɗa min ta waya na ce miki ina da wacce nake so dan har manya sun shiga maganan, harda ke a kazo rakiya kenan." ya nuna Kandy da jikinta ya yi sanyi ta na tsaye kamar babu laka a jikinta ita ma muryanta ra wa yake yi ta ke faɗin " Uncle Umar I'm so sorry please ba za mu sake zuwa ba." "Shut-up." ya da ka wata tsawa sannan ya kalli Fancy ya ce "Miƙomin wayar can." ya nuna wayan da ta cillar, da sauri ta ɗauki wayan ganin har yanzu kiran na tafiya domin ba ta katse mai kira saboda baya so, yasan ta ji komai kuma ta na kusa da wayan yasa ya sa ke ce wa "bata haƙuri." da sauri ta kai wayan ƙunnenta ta furta "Ki yi haƙuri." ƙet ta katse kiran da ga can, abin da ya ɗaure mata kai shine ganin hotan ƴarinyar da kwanaki suka yi rigima da ita a cikin gidan su, miƙa mai wayan ta yi ya amsa, tsaki yaja ya shige bedroom dinsa, ya na shiga Fancy ta kalli Kandy ta ce "Ke hotan wannan ƴar talakawan ce." "Wace kenan?." ta tambaya dan ba ta gane wacce ta ke nufi ba, sai da ta janyo hannunta suka fita sannan ta ce "Ƙawar matar Boss, wannan Ramlat din." " Ke bar wasa." "Wallahi ita ce hotan ta ne a wallpaper, yanzu ha ka muje gurun matar Boss na amsa number ta wallahi za ta sa ni." Fuuuuu suka shiga Main parlour, Aunty da Momcy ke hira suka wuce su, Knocking suka yi ba'a buɗe ba kawai suka buɗe suka shiga kansu tsaye. END Daga alƙalamin Pretty SK. [6/16, 19:54] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9ᑭᖇᗴTTY ՏK https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ❤(。◕‿◕。)❤ [ᑭᖇᗴ𝙏𝙏𝙔 Տ𝙆] ❤(。◕‿◕。)❤ ꜱᴀᴋɪɴᴀ ᴀʙᴅᴜʟʟᴀʜɪ Page 20 ************ ********* A lokacin Ramlat zaune take suna hira da ƙawarta, har tana labarta mata, amma ba ta shedi wacece ba sai dai Kifayaty ta na tsammanin Kandy ce amma ai tana soyayya da Adam abokin Babban yaya. Jita yi an shigo ko izini babu, ɗaga ido tayi tana kallon Kandy da Fancy " Lafiya kuka shigo mun babu sallama?." " Lafiya ce ta kawo haka." Cewan Kandy ta na jijjiga da ga tsaye bakin ƙofa "Okh sannunku." Ta faɗa tana typing da "to jama'ar ki sun shigo,"' sai ita Ramlat ɗin mata reply da "Hehehe, ba na kiraki Voice call." Take wayan yaɗau Ringing aiko ta amsa kiran tare da sawa a speaker ta ce " Namesake fatan kina lafiya?." " lafiya lau friendy, kinsan kuwa gobe za'a sa rana." " For real ?.' "In sha Allah." " Allah ya sanya alkairi." Kallon su Fancy ta yi wanda sun ƙulu iya ƙuluwa kuma har ila yau suna tsaye kaman sojoji, basa son ɗaga mata murya domin Babban yaya jiya ke kaman aljani komai sa ni yake yi, tsaki Kandy ta ja ta fice, dan idan ta na kallon Ramlat ji take kaman ta kashe ta, ita kuwa Fancy matsawa ta yi gab da Ramlat ta ce "Kifaɗa ma ƙawarki ta fita harkan Zaki, ba sa'an auranta ba ne." dariya Ramlat ta hau yi ta ciki wayan dan har yanzu yana hannun Ramlat ne, cikin ƙuluwa da fusata ta fice bayan ta yi ƙwafa sai Ramlat ta ce "Ke ƙawata kinsan yaran nan basu da kunya balle wa'innan biyun." "Share kawai, zan ma Zaki magana." ta ba ta amsa cikin ainiyin voice din ta ba na rigima ba, " Bara na barki zanyima Baby abinci." " Uhmmmm masu baby, Ya kamata zuwa yanzu muji rabo ya shiga amma ƙawata shiru nake ji, Maryam da Hajara abu ya kan ka ma." murmushi ta saki sannan tabce " Ke ai nake jira kiyi auran sai mu jera kawai." "Ha ba Pure white." "Da gaske pure black" dariya suka kwashe sannan suka yi sallama da kashen kiran, ta na tina suna yara suka sa ma junan wannan sunan, ita saboda hasken ta sai a ce pure white, Ramlat kuwa Pure black, aje wayan ta yi sannan ta nufa Kitchen ta hau aiki. ************ ************ Yana kallon komai a cikin na'uransa, jiya yi ransa ya ɓaci sosai, hakan ya sa a fusace ya miƙa, sai kuma ya furzar da iska mai zafi sosai tare da sakin shu'umin murmushi ganin komai yana tafiya yadda ya tsara, a Wheelchair ya sauka ya fa tafiya har wani ƙarin lungu wanda ga ba ɗaya files ne aciki kuma step by step suke, na farko ya janyo ta re da dubawa na wani ɗan lokacin sai ya mai da, ba ya ya koma ya kalli muta ne biyun da ke zaune Spider da Skiddo ya ce "Skiddo yadda na tsara haka komai ze tafi, babu yadda zasu gano mu domin kai ne me bincike akan mu, kawai juya musu tinanin zaka yi, amma a zahiri mu kake ma aiki." faɗin Boss sai Skiddo ya yi magana shima cikin ladabi sosai "In sha Allah, sai dai matsalan shine ba ze yuhu na zauna a family house dinku ba, na ga wannan police din a ciki gidan nan ya ke, kar ya zargi wani abu, and matar ƙaninka ita ma police ce suna da kaifin tinani." " Wannan ba matsala ba ne, kawai a ɗalin Adamsi za ka zauna ƙanuna kunsa ba da shi, kaga ne ai kasa mu free ba yanzu ba ku ke sato hanya ba." da "To." suka amsa, take aka tuɗo ƙofa aka shigo sun san wanene domin su kaɗai ke da ikon shiga wannan ɗakin sirrin na su a haka wannan ƙarami ne meeting na gaggawa ne kawai suke yi. "Boss na ga ma bincike a kan pastor John Johnny, ya na zuwa church duk ranan Sunday in babu damuwa a wannan lokaci zamu iya wuff da shi." "Okh hakan ya yi ma, kowa ya duba wayansa." take suka fiddo wayoyinsu, duk sati biyu suke canza sim, amma su na da number juna wanda su huɗu kawai ke da na juna sai wasu ƴan team din su. "Na turo muku albashin ku, sannan Adam a tabbatar kuɗin nan ya isa in da ya da ce." Da kaiwa nan be jira godiyar su ba ya wuce, su kuwa sunata murna duk one week ake biyansu five hundred thousand, kuɗin ma yawa yake musu, cikinsu duk sun mallaki abubuwa da yawa da kuɗaɗen amma a ɓoye suna jiran lokacin da komai ze lafa ne kawai, duk da haka akwai masu yi musu aiki da yawa su dai duk 2weeks ake biyan su. END ❤(。◕‿◕。)❤ [ᑭᖇᗴ𝙏𝙏𝙔 Տ𝙆] ❤(。◕‿◕。)❤ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ [6/19, 05:40] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: . ❤(。◕‿◕。)❤ [ᑭᖇᗴ𝙏𝙏𝙔 Տ𝙆] ❤(。◕‿◕。)❤ Ka yawaita ziyarar asibiti, insha'Allah zaka zama mai yawan Godiya ga rahamomin da Allah yai maka. True love may be hard to define,but the signs to read true love can be clearly seen in every loving relationships. [6/24, 17:41] Ameeratul Khairy❤️❤️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ☮▁▂▃▄☾ ♛ [Sakina Abdullahi] ♛ ☽▄▃▂▁☮ ᑭᖇᗴ𝙏𝙏𝙔 Տ𝙆 page 21 *********** **************** Kandy na shiga part dinsu, ta nufi ƙofan ɗakinsu ta shiga, zama ta yi tana jin tsanar Ramlat biyun nan, babu wanda ya tambaye ta sai da Fancy ta shigo tana hawaye shine suke tambayi ba'asi sai Kandy ta faɗa musu, suna ta mamakin ƙarfin halin Fancy domin Zaki sam ba shi da wasa haka rayuwansa yake ɗan zafi-zafi ne. "Shi ya sa na tsani talakawa har kwanda matar Boss, hmmmm samun waje, wato ta shiga ɗaula bara ta jawo ƙwarya." Cewan Besty ta na yamutsa fuska sai Beauty ta caɓe zancen da ce wa "In da ranka kasha kallo, ta kula ranan da za ta shigo hannunmu." " Ni ban ga wani abu a ciki ba a.i" " Baby shut up, dan ƙanin Aunty ne ko dole ki yi magana ai." Cewan Beauty ta na hararan Baby. "Ku dai bar maganan yanzu dai zuwa gobe za mu faɗa masu Pazars kawai." "Gaskiya Husty ba ki da sense, wani ya ji abin nan ai mun shiga uku." Cewan Hasty sai Karis ta ce "Ai kuwa dai wannan shine son wani ƙoshin wahala." da ga haka suka bar zance amma Fancy har 1am na dare idonta biyu, kira ne ya shigo wayarta amma baƙon number, amma ta na ji kaman Babban yaya, kiran har ya katse sai ga saƙon ya shigo ta kalla na kusan minti 5 wanda aka rubuta. "Damuwa ce ta hanaki barci, love ki ka shiga hmmmm, na ba ki 10mnt da kiyi barci kuma gobe zamu haɗu da ga Boss." Da sauri ta a jiye wayanta kwanta cikin ikon Allah barcin ya ɗauke ta. *********** ************* Ko da ya gama komai a cikin wannan ɗakin nasa na sirri, sannan ya fita zuwa gurin matarsa, daƙin ta ya shiga yasa mu ta na barci, ha wa gefan gadon ya yii ya na kallon Beauty face dinta me sheƙi da annuri, ya rasa me take ci da sha kwana biyun nan ta ƙara kyau da jiki, ga skin dinta sai glowing shi ma yake yi, ji yake kaman ya mai da ta cikinsa sa boda tsananin ƙauna, ya na sonta kuma ya na kishinta dan ko da wasa ba ta fita ba tare da ta kulle ko ina na jikinta, sannan ga muta ne biyu masu kai ta da jiranta a iya saninta amma a zahiri kuwa su goma ne har da mata wanda suke a aji ɗaya, haka duk ka ƙannansa kowa ya zuba mai secret guards like 5 people, haka su Pazars ma, sai Aliyu Haidar wanda na shi yafi na kowa sa bo da aikin daya ke yi dan wa'innan securitys din duk ya musanya ma su, harta matarsa Meerah be bar ta ba ita ma yasa mata dan akwai abubuwa da ta ke fuskanta a kan aiki. Ganin barcin nata ya yi nisa ya sauka a Wheelchair dinsa ya miƙa tsaye, in ya dawo RASH komai na sa sauyawa yake yi, freezer ya buɗe na ɗakinta ya dauka drink me sanyi ya koma kan sopa ya buɗe yana sha tare da buga wa brain dinsa lissafin wasu abubuwa, a nan gurin barcin ya ɗaukesa. ****************** **************** Kwana biyun nan ba ta jin daɗin sosai hakan ya sa jiya taje asibiti dan a du ba ta, kwajin farko aka samu ta na da juna biyu, ta yi farinciki sosai ma ra misaltawa, sai dai me bayan Aliyu ya dawo da ta faɗa mai shi ma yaji daɗin fi ye da na ta sai dai a in da matsala take shine ya ce tin yanzu ta fara neman hutun gurin aiki dan sau biyu za ta dinga zuwa a week nan ga ba kuwa dole ta haƙura ma, abin da ya sa yau duk ta bi ta haɗe fuska, ta san baya cin taliya aikuwa shi ta da fa, mai da yaji kuwa, kallonta kawai yake yi yasan neman rigima take yi aikuwa ya ɗaure ya ci har da ce wa ya yi daɗi, ba haka ta so ba ta so ya yi complain ta hau masifa sai ta ga ya basar duk da tasan ƙarfin hali ya yi gurin ci, ta rasa me ya ka mata ta yi wanda shi ma za ta ɓa ta masa rai, bedroom dinta ta wuce ta yi kwanciyarta, shi kuwa sai da ya kai 12pm ya na kallo da ga bisa ni ya gyara kwanciya akan sopa sanyin A.C na ratsa shi, ko da cikin dare ta farka sai ta fito a can parlour ta hangesa sai ta koma ta ci gaba da barcinta, ko da gari ya waye bayan ta idar da salla ya higo dan su gaisa kawai ta haushi da faɗan ƙarya, faɗan da babu gaira babu dalili wai dan ya kwana a parlour. "Wato barci kasha, ko damuwa da ni baka yi ba, hmmm ya yi kyau sosai, haka jiya ka gama cin abincin kabarmin kwaninka agurin na gode." Ta kainan tana cire hijab din jikinta, kallonta ya yi sai ya share yasan jira take yi ya kula ta su hau tuhuma dan shi be ma ta ɓa ɗauke kayan abinci ba idan ya ga ma ci sai dai ranan da shi ya dafa, sannan ta da sa da ce wa. "Wato ina magana ka share ni, ni wai....." duka iya ƙarfin sa ya sa ya janyo ta, ta faɗo jikinsa ba tare da ta gama maganan ba. "Ashhhh za ka karya ni, na san baka sona yanzu ai." nan ma be ce ko ƙalaba sai da ya ɗauki minti 10 a haka, sai ya kai ba kishi saitin kunnan sannan ya ce "Gaba ɗaya week din nan ki na gida babu inda za ki....." ta yi saurin to she mai bakinsa tare da marairaice fuska ta na ce wa "Uhmmmmm ni ban son na ɗauki hutu da wuri, nayi ma alƙawarin duk ranar da muka gama case din Rash zan ɗau hutu sai time to time zan dinga zuwa, amma be ka mata ka ce za ka hana ni zuwa ba." "Na ji kinga sai kusa mu ku yi da wuri dan da yarona ya yara zama mutum ba zaki ɗaura mai pressure ba." "Toh, amma ka taya ni da addu'a kawai duk da binciken ba'a samun ci gaba ko kaɗan, ga lokaci sai tafiya yake." da ga haka suka shiga wani hiran daban na su na masoya. END ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ [6/24, 17:41] Ameeratul Khairy❤️❤️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Page 22 **************** ************ kamar kullum in ya zo kwanciya sai sun yi waya da babynsa amma yau tin da zu yake kira ta ƙi ɗauka, ya san duk yaran can ne suka sa ta yi fushi, gashi gobe su Pazars za su je su kai sadaki da tsaida rana, ya so ƙananan baban shi su zo daga Abuja, amma Pazar Q ya ce ba sai sun zo ba, damuwa duk ya'ishe sa, hawa online ya yi da mamakinsa ya ganta a online, 'Slm' ya yi mata sai bayan 2mnt ta yi mai reply da "wslm." sai kawai ya kira ta voice call dan ba ta ɗaukan video call ba, haƙuri ya fara ba ta, sai ta nuna babu damuwa da haka suka dinga hiran yadda rayuwan su na aure ze tafi dan Ramlat ba ta ɗaukan abu da zafi balle ma ta sani Lion dinta yana son ta sosai "Baby ki zaɓa a ina kike son mu zauna?, a nan familyn ƙanƙara tin da akwai part part dan haka Pazars suka cemin amma in kina so zamu iya neman wani gurin na, so can Abuja zamu koma amma babu dama da yake acan ɗin ina da gida gadon babanmu.' ai kaman ta na jira ta ce "A nan dai yafi kodan ƙawata ka ga ni." amma a zuciyarta ta na cewa ko dan ta nuna ma su Khadija, ba a zaginta a zauna lafiya, gashi akwai ya da mugun riƙo, da haka suka yi sallama suka rabu bayan sun sa ƙauna sosai. ************** ************** A yau 9 wednesday\4\2025 misalin 11:33am, abin da ya faru ya hargiza muta ne da yawa domin yara ɗaliban ilimi, kuma zallan ƴan mata su talatin (30) a wannan babban makaranta nan wato EVANT INTERNATIONAL SCHOOL, wacce ke cikin hajar Kaduna, makaranta mai ji da kanta domin duk yaran masu hannu da shuni ne a ciki, tin jiya a ka kwashe su duk da ba'asan taƙa maiman lokacin da aka kwashe su ba, sannan iyayen yaran sun kai ƙara gurin jami'an ƴan sandq harta hukumar makarantar ta shiga alhini, abu mafi razanar wa shine a safiyar yau 11am sai ga video an saki na RASH kan cewa garkuwa ya yi da su kowa ya shirya kuɗin fanasa, gaba ɗaya muta ne cikin zullumi suke ballan tana wa'inda ba suga yaransu ba. harta shi wanda ke zaune yana kallo a T.V baya cikin tsaro in dai a wannan ƙasar ne, muta ne suna tsoron kar ƴan matan su shiga matsala domin duk kan babu wacce suka haura 20yrs, kuma abin mamakin shine kallaman da ake kira RASH ya faɗa kan biya kuɗin fansa." Matashin saurayin da ke cikin maginin TV ya gama kowo rahoto cikin alheri kuma ta je suka canza shirin zuwa wani abu, Shuraim da ke zaune ya na kallon tunani ya shiga yi mai zurfi dan sai da Kifaty ta na yi magana a karo na biyar shine ya dawo da shi cikin tunaninsa. "In sha Allah a sirin RASH ya na gab da tonuwa, kwana biyu ya bar kisan shine ya koma satan yara mata, Allah ya sa babu abin da ze musu." Sai ga hawaye sharrrr ta mike ta nufi part din ta, be da katar da ita ba har ta shige, ya rasa meke mai daɗin be ma bi takan Wheelchair dinsa ba da ƙafafuwan sa ya nufa na sa ɗakin ta re da kira a waya bugu biyu aka ɗauka "Ina son ganinku yanzu nan." Ya kashen wayan yana murɗa handle din ƙofan sannan ya kukkule ko ina tare da nufan wannan lungun, already sun iso dan jin labarin da ke yawa a media su kansu sun san akwai meeting na gaggawa. ya na shiga ya zauna ya na faɗin "Kunga me ke faruwa ai, ina son na sa ke ganin wannan video din da a kace an saki." take Spider ya kunna flash tare da so ka wa a magic TV, sai hotan ya bayyana mutum ne sak me irin shigan da Shuraim yake yi yana zaune sai ya miƙe ya fara tafiya tare da yin alama da hannu sai ga yara mata su talatin, dukkansu suna sanye da Uniform iri ɗaya amma duk an rurrufe masu fuska, magana ya fara yi da irin muryansa sak "Nasan kun san Ni wane ne, to ko wani mutum ɗaya a cikin yaran nan za su bani number ɗaya daga gidansu tanan ne zaku biya kuɗin fansa, nabarku lafiya da ga ni RASH." Ƙet Videon ya ƙatse, gaba ɗayan su shuru suka yi suna mai tinanin waye wannan da ke neman sa kanshi a hatsari sosai, sau uku Shuraim ya kalla videon sai ya saki shu'umin murmushi ya na mai ce wa "Ɗayan biyu ne ko dai plan ne jami'ai suka haɗa domin kamani kodai wani ne ya fito domin samu kuɗi da sunana." "Boss yanzu yake so ayi, in kace zuwa gobe mu binciko sa zamu kawo makashi." Cewan Adamsi cikin haɗe fuska, sai Skiddo shima ya ce "Haka ne Boss, aiki nan ko wani kalan hatsari ne mu masu shiga ne balle a kanka RASH kai ne gatan mu na duniya da Allah ya ɗaura maka." "Ga duk kan alamu koma waye sunyi dubara da kuma sunyi ƙoƙarin dan harta muryata sun ɗauka sai dai ga dukkan alamu na ɗan fishi tsayi amma zamu samo shi, kubari muga iya gudunsa kawai." daga ha ka ya fice suma suka fita, ko da ya hau kan bed dinsa sai ya tina be ɗauko Wheelchair dinsa ba nan take ya ti na ɗazu da safe da suka tashi da ga barci ''''''' Muryan ta ne ya doki kunnansa ta na ce wa "Baby ya aka yi ka iya zuwa kan sopa ba tare da Wheelchair dinka ba?." Ko da ya watstsake sai ce mata ya yi. "Keken ai me tafiya da kanshi ne idai an danna to shine yake matsawa." Bata kuma ce wa komai ba kuma ta yadda 100%,''''''''''' Amma be san me ze ce mata an jima ba, dan ba ya yana yin da ze iya fita yanzu, cikin sa'a barci ya ɗauke shi bayan ya kwanta. END. ❤(。◕‿◕。)❤ [ᑭᖇᗴ𝙏𝙏𝙔 Տ𝙆] ❤(。◕‿◕。)❤ [6/25, 13:01] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Page 23 ********************* Jami'ai duk hankalin su a tashe yake tun ganin me ke faruwa, an rarraba jami'a duk gidan da aka yi garkuwa da ƴarsu, gidaje 22 ne don wasu yara biyu ne a gida ɗaya suke, zuwa yanzu har an biya kuɗin fansan mutum 6 ta wani account a GT Bank sai dai be da suna, 1M ne a ka cazi ko wani yaro, harta GT bank su Zaki sunje amma basa'a domin ana sa kuɗin ake cire wa a take, sunata binciken POS din da ake cire kuɗin amma basa gani, hakan ya ƙara tabbatar musu da RASH mayen na'ura ne, sam ba su da sa'a a haka har sai da aka gama tura mai kuɗin duk ka dan RASH ya ce cikin 3h yake so a gama biya shi ya sa kowa ya samu ya biya, yanzu a nata jiran sakon yaran dan a tare suka ce zasu sake su, sun san jami'a na an kare amma idan Allah ya so taimakon mutum cikin ikonsa da buwayarsa ya na taimako. Misalin 12pm na dare, babban mota ta nufa cikin gari direct makarantan EVANT INTERNATIONAL SCHOOL suka nu fa sannan suka shiga dan sun sai ta komai da shigansu cikin baban makarantar wanda babu kowa a ciki, fitowa wasu muta ne biyu suka yi daga motan suna sanye da baƙaƙen wando da riga, ko ina nasu a rufe, haka suka nufa hanyan fita amma da takun farko na biyu na uku, suka ga an zagaye su tare da danjan bindigu ajijunsu dan haka suka ɗaga hannayen su sama ƙirjinsu na matsanancin bugu, polisawa su suka rarratso ta a ina da suka ɓoɓɓoye, Zaki ne a gaba har hamdala yake yi akan yau sun samu nasara cafke RASH cikin jin daɗi ya ba da umarnin banda harbi sannan ya matsa jikin babban motan sannan ya sa wasu suka buɗe take ya hangi mata duk suna sume........... ******************* **************** Cikin barcinsa ya jiyo a na buga ƙofansa a haka ya miƙe ba tare da tinanin komai ba ya nufa ƙofan hannu ya sa ya cire gaba ɗaya lock din da ke jiki, sannan ya buɗe, ganin ta ya yi tsaye tare da Wheelchair dinsa, fuskansa a matuƙar haɗe take babu annuri kuma babu rahama, kallon-kallon suke yi dan ita suman tsaye ta yi ganin gurgun mijinta a tsaye da ƙafafunsa magana take son yi amma kalmomin sun maƙale a maƙoshinta baya-baya tafara yi cikin zafin nama yaruƙo hannunta aikuwa ya cafkota amma sai da ta suma, ɗaukan ta ya yi cak kaman baby ya nufa Parlour kwantar da ita ya yi kan kujera sannan ya ɗauko ruwa a fridge ya yayyafa mata cikin ikon Allah sai ta farka suna haɗa ido ta zabura tana miƙewa daga kwanciya ta na ce wa. " Dama kana ta fiya ne?." ya ɗaga mata kai yana zama a gefanta, gaba ɗaya duk ta ruɗe zabura ta kuma yi tamiƙe dan nufan ɗakinta, yasa hannu ya mai da ta ta zauna juyowa ya yi suka fuskanci juna ya na ce wa. "Ban san magana, and ban san tambaya." abin da ya ce kenan sannan ya miƙe ya nufi room dinsa da idanuwanta ta bisa ta na kallon yadda ya ke tafiya cikin natsuwa, a yau take ƙare mai kallon, yana shiga be jima ba ya fito ɗauke da magani, kallonsa take yi ko ƙyafta ido ba ta yi, gashi besan riga ba wannan faffaɗan ƙirjinsa na waje mai ɗauke da yalayalan baƙin gashin da suka kwanta. "Wannan kallon fa, na mene ne?." Ya na furtawa ta ɗauke idonta ta na mai tinanin iri-iri a ranta, maganin ya ballan mata aikuwa ta amsa ta sha, zama ya yi ya na mai ce wa. "Na yadda da ke, ni dama ainiyin ba masaki ba ne lau na ke, so na ke kiriƙemin wannan sirrin sannan na lura ki na da brain sosai ina son na baki wani aiki ne." Jita yi kaman mafarki take yi sai ta ce "Pleasr ka ta dani da ga mafarkin da nake yi." Yadda leɓen nata suka matso sai yaji har zuciyarsa domin irin me pink lip din nan ce, ba ta an karaba sai ya haɗe ba bakinsu guri ɗaya ya hau kissing na ta cikin rashin sabo, a hanli ya za me bakinsa ya na ce wa. "Bansan tambaya yanzu kin yadda a zahiri kike koh ?" dasauri ta ɗaga kanta tana mai taɓa bakinta danjin ko yananan. miƙewa ya yi ya koma ɗakin na sa ta bisa da ido kawai, can sai gashi ya fito da wani trolley a jewa ya yi ta re da ce ma ta "Kule ƙofofin gidan nan." da sauri ta miƙe ta nufa ƙofan fita takukkule harda ƙafan da ze sa da ka da Main parlour, isowa in da ya ke ta yi, ya mata nuni da in da za ta zauna aikuwa ta zauna babu musu, buɗe jakkan ya yi ya fiddo na'urori kala-kala take ya haɗa wanda ya keso ita dai bin sa kawai ta ke da ido, ta ke wayansa ya yi Ringing janyowa ya yi daga gefan Pillow ya ga Adamsi, yana katsewa ya kira sai ya ɗaure, speaker ya sanya sai ya ajiye a gefan sa sai na cikin wayan ya fara magana. "Boss abubuwa na ta ta'azzarafa, a halin yanzu 1million for each person." kaman Shuraim ba ze ce komai ba sai ya ce "Karku da mu kubarsa zan haɗa mai tarko kawai kudaiyi sab gan gabanku kawai." ya na cewa haka ya katse kiran tare da kallon Ramlat wacce ke kallon shi ita ma, murmushi ya yi mata mai sanyi, ta mai da mai da yaƙe, operating system ya fara yi cikin kwarewa, sannan yace ta musu girki haka dai suka wuni yana aiki da na'ura ita kuma tana kallon yadda yake yi sai 7pm ya ɗauki wayansa tare da kiran wani number bugu biyu aka ɗauka. " Zaki." "Na'am Babban yaya." "Kunna location na ka zan ha ɗaka da wani red light karkuyi komai sai idan sun fara tafiya sai ku bi su amma hakan ze sa su gane, nan da 1h zan kajini, before the time make sure get ready." " Godiya mu ke Babban yaya.", ya katse kiran, Ramlat ya bawa wani abu ya ce ta yi ta matsa shi aiko shi ta ke ta yi, zuwa na 9pm ya kuma kiran Zaki. "Ku nufa EVANT INTERNATIONAL SCHOOL, cikin shigan kayan gida, kuɓoye motocin ku, idan kunje sai ku sauya me gadin sannan kumai dubara dan ɗan team dinsu ne, idan kun shiga ku ɓoye har sai sun zo." Be jira me Zaki zai ce ba ya kashe wayan tare da kwanciya kan sopa sannan ya ce "Ya isa matsawan ki barshi haka." aiko ta tsaya dayin, miƙewa ta yi ta shiga ɗakinta ta rufe, lumshe idanuwansa ya yi dan ya gaji sosai da ƙar ya samu makama, ita kam tana shiga ɗakin zama ta yi jikin gado ta na mai tinani wai ce wa ya yi "shi dama lau ya ke ba gurgurba." Abin ya tsaya mata kodai warkewa ya yi, ganin tinanin ze cutar da lafiyanta ya sa ta shiga toilet ta ɗaura alwala. END. ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿. [6/25, 13:01] sknt6428: 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ Typing..... page 24. *************** ***************** Ganin sun shiga tarko ba yadda za suyi haka suka tsugunna har polisawan suka yi ram da su, sannan aka kawo mota a ka sanya su, station aka kai su anan suka tadda ƴan jaridu cike da gurin suna ɗaukan rahoto, aka dinga video jama'a cike da gurin, a nan babban motan da ƴan matan ke ciki suka iso, Amma duk suna sume ganin haka aka shiga dasu Asibitin da ke opposite da station ɗin, gurin yadda kasan rana sa bobda muta ne, cikin sa'a yaran duk su na ƙoshin lafiya, kawai maganin barci suka ba su. sannan iyayen yaran sun zo, Zaki su ka ma godiya sannan suka fucye, an yi an yi aga fuskokin muta ne biyun nan amma abu ya gagara kawai wani ɗan tsoho ne wanda fuskansa ke bayyane, sai misalin 4am na safe aka watse ya rage a station din muta ne kaɗan ne masu night duty ne kawai sai Zaki da ke office din Ramlat wanda yanzu tare suke sharing ɗin, Ita dai ta leƙo ɗazu ita da mijinta sannan suka wuce. miƙewa ya yi ya nufe cikin cell din tare da shiga, yana shiga suka ɗago suka kallon sa zama ya yi kan wani kujera tare da kallonsu yana mai cebwa "Zuwa safiya zamu miƙa ku kotu, muta ne da yawa suna son ganin fuskokin ku, amma na hana sa bo da wasu dalilai na, ba na buƙata jin komai da ga bakinsu illa kushirya tambayoyin da zaku amsa, bazan ɓoye muku ba, direct kashe ku za'ayi, yanzu address ɗin ku nake so domin kwaso evidence da bincike." shuru babu wanda ya yi magana sai ɗayansu ya fara shashsheƙan kuka a hankali cikin wani yanayi mara daɗi, take kuma muryan me kukan yafa ainiyin bayyana, muryan mace ce, murya mai taushi, murya mai daɗin sauraren kaman busan sarewa, ji ya yi kukan na taɓo ƙashin ranshi amma abin mamakin wai da ma mace ce ita ko dai ya ne, be gama tinani ba yaga ta na fincike baƙin abinda ta sanya wa fuskanta, take zuciyarsa ta buga da matuƙar ƙarfi, haɗe hannunta ta yi tana mai jan gwiwowinta zuwa gaban shi, rigo ƙafafunsa ta yi tana kuka mai shiga rai, gaba ɗaya Zaki ya rikice sosai, ya rasa me ya kamata ya fara yi shin ya sa ta tsai da kukan na ta ne ko ya ɗauki wayansa ya kira budurwa sa domin ƙaryata abin da ya ke gani, da sauri ya finciki ƙafarsa tare da ficewa daga cell din ya na jiyo ta saki sabon kuka amma be bi ta kantaba ya shige office dinsu yana ɗaukan wayansa, ƙirjinsa sai zafi yake mai. ( Toh fa, Zaki how far?.) ***************** ***************** Cikin barcinta ta jiyo wayanta na Ringing kaman ba zata motsa ba jin dai sai kira ake yi ya sa ta miƙe da ƙyar, ɗaukan wayan ta yi wacce ke jikin charging ganin sunan My ASAD ya bayyana ya sa ta ɗauka tana mai kai wayan kunnanta "Asad dare ne fa fatan kana lafiya.?" abin da ta furta kenan sannan ta aje wayan dan ya katse. ɓangaren Zaki kuwa kira ya dinga yi, ya kira sau 10 tukun da ta ɗaga, tana magana yaji hankalin sa ya kwanta sosai sai yace "Oh sorry Queen sai da safe." sannan ya kashe kiran yana mai ganin irin ikon Allah fita ya yi yana mai hangen waccan, wacce ke ta rusa kuka, idan badan yanzu yaji muryan Ramlat ba wallahi ze ce ita ce waccan wadda ke kuka, kamarta su tayi mugun ɓaci kaman an tsaga kara, harta muryan ta ya ji iri ɗaya ne sak da Babynsa, cikin dauriya ya koma cikin cell din, da jajaye idanuwanta ta kallesa wanda hawaye ya cika su, tsohon nan wanda a ƙalla ze kai shekaru 60 ya ce "Sakeenat ki yi mana shiru, da me za muji ne wai.?" "Kahu ya zanyi toh? shike nan zasu kashemu gobe." sai ta ƙara rusa kuka sai a lokacin ɗayan wanda suka yi shiga iri ɗaya, ya yi magana da muryasa wanda hausan nashi ma ba ya wani fita kaman na tsohon. "Na ja ma na,, tsautsayi ya faɗo kanmu, gashi mu shiga cikin matsala." sai ya kifa kansa ya na kuka ciki-ciki. Zaki na da tambayoyi akan su amma ya rasa ta ina ze fara domin sunƙi natsuwa ma balle su yi shuru, zama dai ya kuma yi ya na binsu da kallo na kusan 15mnt, duk sunyi shuru sai ya buɗa bakinsa ya na ce wa. "RASH masheƙi, ina so na ji tarihin rayuwan ka, ina son nasan dalilin da ya sa ka zaɓi kashe muta ne da garkuwa da su." "Ni suna na Mus'ab ba RASH ba." Matashin yaron ya furta tare da cire mask din fuskansa, sai kyakkyawan bafullatanin fuskansa ya bayyana mai kyau dai-dai misali. "To wane ne RASH? Ku ma'aikatan sa ne?." a ta re suka girgiza kansu wanda ke da ma'anoni da yawa. END ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿. https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Typing Page 25 ****************** *************** Tinda asuba ta shirya bayan ta idar da sallan subh, fa yake abu ne da ya shafi kowa da kowa dan direct wanann case din sai Supreme court na Abuja wanda za'a shiga 11am na safe, shiryawa suka yi a tare suka nufa station ɗin da jagororinsa sun isa 7am amma muta ne a gurin kaman a nan suka kwana, ba su yi mamaki ba sa bo da wanted aka ka ma, ko da suka samu suka shiga, kulle gurin a kayi dan an hana kowa zuwa in da suke sai Zaki, amma ganin gomman garin Kaduna wato His Excellent Aliyu Haidar Abdulqadir ƙanƙara da matarsa ASP Ramlah ya sa suka shiga a tare, ganinsu suka yi tare da fitowa bayan ɗan lokaci. " Yanzu wan can farin yaron shi ne RASH, it's impossible ba shine ba." Ramlah ta faɗa tana da fa kanta, har ranta ba ta yadda wancan shine ba sai dai idan ɗaya daga cikin yaron RASH ne, domin shi mutum ne mai basiran gaske, ba haka ta ke hasashen ganinsa ba, ba haka idanuwanta ke mata nuni ba. " Omry kar kice haka ba ki da hujja ki bari ayi binciken a gani." "Ha ba Farsi, ko barci na tashi ba zan yadda wannan yaron ɗan 22yrs shi ne RASH ba duk da suna sauya murya amma ina." sai a lokacin Zaki shima ya yi magana. "Kwarai wannan ba shine RASH ba, amma ya yi wasa da rayuwansa kuma ya ta ka sahun ɓarawo." take ya basu labarin abin da Mus'ab ya bashi, jikinsu ne ya yi matuƙar sanyi, duk sun sha yarinyar can Ramlat ce ƙawar matan Baban yaya sai da ga baya suka fahimci me kama da ita ce sosai, hawaye ne ya zubo a Idonta, ta share ta na mai ce wa "Yanzu abu ɗaya ne ze sassauta hukuncin da za'a musu agun alƙali." Aliyu da Zaki suka kalleta suna son ƙarin bayani sai ta ci gaba da ce wa "Idan har RASH ya kuma aika ta wani mugun aiki, hakan ze sa muta ne su yadda da zancen wa in nan yaran". "Haka ne amma na dai ce su dage da addu'a kawai." daga haka suka yi shuru sai jin Knowking suka yi, Zaki yama san waye dan haka ya ce "Coming." wani Police ya shigo, sai da ya gaidasu sannan ya ce "Sir mun haɗa komai yanzu than the flight is ready." "Okay." kawai ya ce sanann mutum ya fita bayan ya ƙara sa ra musu. Aliyu da Meerah fita suka yi suka shiga mota, sai aka fito da maza biyu wa'inda aka rurrufe musu fuska aikuwa nan take a ka hau ihu da jefe-jefe, sannan ƴan sanda sun kewaye gurin har kokawa aka dinga yi suna shiga mota aka tada nan fa motoci suka bi su aka ɗauki hanyan zuwa airport, muta ne duk suka bisu balle ƴan jaridu kaman mayu haka suke wani lokaci. *************** **************** A cikin station kuwa da har ta miƙe sai ta ce "Sir ina son na yi fitsari." jin ta ce haka ya sa ya ce su Meerah su yi gaba da mazan shi ze ta ho ta ita, aikuwa haka aka yi suka tafi shine ya zauna yana jiranta hatta fito, a lokacin babu kowa a office din sai shi, kallonta yake yi cikin matuƙar mamakin, gani yake komai nasu iri ɗaya, harta yadda suke yin magana sai dai wannan tafi Babynsa boko, wando ne jikinta na jeans baƙi haka rigan ma basu kamata ba dan babu mai gane ita mace ce, doguwar ce kaman Ramlat dan kaɗan ne ya rage ta kaishi, tana zuwa dai dai shi ba ta an karaba ruwan daya zuɓe ɗazu na bottle shine santsin ya ja ta za me wa ta yi hatta rufe Idonta dan tasan faɗin za ta yi, sai taji ba ta faɗiba, sannan ta ɗari ji an finciko ta, hannayen ta ya janyo, kallonta yake yi irin kallon ƙurillan nan, ba su da ma ra ba da Babyn sa sai dai idan an gansu a tare hala a sa mu different, a hankali ta janye kanta ta na mai ce wa "Sorry ban san akwai santsi ba." kai ya ɗaga mata alaman babu damuwa, daidaita kanta yi tana mai janyo abin kulle fuskanta zata ɗaure sai ya janyota gabansa yana kallonta cikin ido, ya rasa me yasa yake jin wani ya nayi akan ta fiye da yadda ya ke ji a kan Ramlat ɗin sa. " Yanzu shike nan kashe mu za'ayi ko?. Sai ta hau kuka sosai har tana durƙusuwa ƙasa, tana leƙan yadda ƴan uwanta suka fita ana ci mutum cin su ita ko sai Allah kawai, hannu ya sa ya rige hannaunta ya na ce wa " Ba kyaso ki mutu ne?." aiko ta ɗaga mai kai alaman eh, ya jima yana kallon fuskanta cikin kuka sai yasa h tare da goge mata hawayen da tissue, a kunninta yaraɗa mata bayan ya tsugunna gabanta har suna shaƙar nunfashin juna. " Karki damu, Zaki na tare da ke yanzu dai ki yi duk abin da na ce in dai bakya so a kashe ki." " ASP zanyi amma su ƴan uwana fa?." "Suma za su kuɓuta In sha Allah, ba komai yasa na tsameki a case din nan ba sai dan hukumar mu ta ba buƙatar irin ki don kama ainiyin RASH, yanzu muje." miƙe wa ta yi suka nufa fillin staion din in da ta hangi mata biyu na tsaye cikin shigan kayan police din, sai da suka je gab dasu sannan ya ce "Ku kai ta in da na umarce ku, sannan ku mata komai da ta ke buƙata sai ku kulleta a ciki." " Ok Sir." abin da su ka ce kenan suka riƙe hannun Sakeenat suka fita ta ƙofan ba ya, a hankali ya sauke ajiyan zuciya sannan ya fita ya hau mota shima ta nufi airport, ko da ya isa sai da ya jira second Flight dan wan can ya cika, da yake babban case ne kuma kowa na so yaje yasa muta ne rututu a gurin cikin sa'a nan da nan second flight ya tashi sai burnin tarayya ABUJA dan har shugaban ƙasa sai ya halicci wannan case din, suna sauka a ya tadda mota na jiran shi aikam ya shiga sai Supreme court. yana isa sai da mamaki ya kusa sumar da shi, wannan babban filin amma tab yake da muta ne har titi, an sanya babban majigi wanda tsaf ake hango muta nen court din, daƙar ya samu ya shiga ciki dan muta ne da ƴan jaridu sai tambayoyi suke mai akan "Shin wani hukunci za'a yanke ma RASH? kasheshi zasu yi ko zaman gidan yari? wane ne wannan RASH din?." duk ya najin tambayoyin amma ya share ya shiga ciki, yana shiga ya kalli jama'an gurin yako ƙara tabbatarwa dole sai Mus'ab da Kahu su fuskanci kisa domin cikin court din shuwagabannin ƙasar Nigeria ne kawai sai tsirarun polisawan da Lowyers. Neman guri ya yi ya zauna yana mai kallon yadda jikin kahu ke rawa na firgici, gefan Meerah ya zauna ya na ce wa "A ganin ki akwai yuhuwar kuɓutansu." ya yi maganan ƙasa-ƙasa. "Eh to a gaskiya babu time dan ya kure sai dai idan an ba su a dadin kwanakin da suyi kafin ratayan da za'a musu in dai ainiyin RASH ya bayyana to hukuncin ze yi sauƙi a ganina, sai a lokacin Alƙali ya buga tasa gudumar dan fara sharia. END 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊 [6/27, 22:00] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Typing Page 26 *********** ********** ************ Ko da jin labarin an yi ram da Rash, ya sa ko wani gidan TV shirin ake haskawa, ba ta yi niyyan fitowa ba saboda haushinsa ta ke ji akan me ya sa yake pretending shi gurgu ne ashe ƙarya ne, jin dai labaran da ake yi ya sa ta fito palourn, a zaune ta sa me sa ya na kallon NTA TV, sai ta zauna a gefansa ita ma ta zuba Idanuwa akan rahotan da ake yi, jin RASH ne aka kama yasa ta ji duk damuwanta sun watse sai ta shiga zagin RASH tare da mai mugayen alkaba'i, ji ya yi duk ta isheshi hakan yasa ya janyo saltape ya liƙe bakin na ta, a haka har suka gama labaran ace wan gobe za'a miƙa su court, tin daga tsayuwan maza biyun nan yasa ya fahimci kaman akwai mace a ciki, dan haka system ya ɗauko tare da datsan na'urorin cikin station din, take ya hangesu su uku a cell, ɗaya cikin irin shigar sa ne jikin sa, na gefan sa dattijo ne mai ɗan shekaru, sai mace wacce ke dungule gurin guda tana kuka mai cin zuciya, tare suke kallon har lokacin da Zaki ya kuma shiga, sai a lokacin yarinyar ta ɗago tana magana da kahun na ta, a tare suka haɗe ido, dan ganin takwararta amiyarta Ramlat, cikin rashin fahimta suke kallon yarinyar, hannu Ramlat tasa ta fincike abin ke bakinta tare da ce wa " Ƙawata, me take yi a station?" sai ta nufa ɗakinta ya san wayarta za ta ɗauko aikuwa tana shiga ta ɗauko ta fito tana kiran number Ramlat wanda ta yi saving da Friend 4 ever, kira ta dinga yi kaman me duk ta ruɗe, sai can aka ɗauka "Ƙawata." Tafurta cikin magagin barci " Na'am ƙa..w.a.t...a." daƙar ta haɗa magan ganun na bakinta "Lafiya cikin wanan daren ba ki yi barci ba?." " Ina fa lafiya, dan Allah hau online na nuna miki abu yanzu." Iya kan jinta ba ze wadatar da ita ba dan haka ta katse kiran tana hawa online, tana shiga sunanta direct ta shiga ta kirata, bugu biyu ta ɗauka, hamdala Ramlat ta shiga jerawa ganin ƙawartata a hankali tana kan katifa ta rufa jikinta da hijab ta ce "Lafiya kuwa na ga kina hawaye? Meke faruwa ne?." " Lafiya dama kawai so na ke nagan ki ne." Ta ba ta amsa tana share wayenta, shi dai Shuraim da ido kawai ya bita har har ta shige ɗakinta, ya san ba za ta faɗa mata komai ba, sai a lokacin kuma wanan yaron na cikin na'uran ta sa ya fara magana bayan ya cire mask dinsa, kaf ya gama jin labarin tare da tausaya mu su, ko da ya gama kallon har da shawaran da matar Aliyu ta ba da akan abu ɗaya ne ze cece su duk yabji. Kashe system din ya hi yana mai tinani iri iri, a gurin ya yi barcin 2h, yana ta shin ya fara gabatar da sallah kafin ya shiga part dinsa har da kullewa yadda ya sa ba. ************** *************** Su na isa gidan in da ASP Zaki Umar ya sa su nan suka kai ta cikin part ɗin da, sannan suka mata komai suka fita, tun shigowansu ta fahimci irin dukiyar da aka narka a gidan, suna fita suka kulleta, zama ta yi kan kujera bayan ta zaga ko ina na cikin ɗakin, wanka ta yi sai ta ci abinci, kunna TV ta yi dan ta na son ta kalli komai da komai, tashan AIT ta sanya wanda ta ke cikin court ɗin ta fara gani alamun yanzu aka fara shari'an ga banta ne ya shiga mugun bugu da ƙarfi, ganin irin tarkon da suka shiga sai ga hawaye ya fara zu ba daga idanuwan ta, da ƙyar ta yi shuru tana jin me alƙali ya ce " Kotu ta yanke hukunci rataya ga mutanen biyun nan, nan da rana ita yau (1 week) a kan baban titin GRA wanda ke kusa da asibitin Zurfi Hosbital, domin kisan su ta za ma izina ga masu irin halin nan, shedu da komai sun bayyana suke yin komai da ke faruwa a cikin ƙasar nan, sannan sun amince da duk laifinsu." Take kotu ta hau hargizi wani na ce wan "yau ya ka mata a kaisu lahira, wasu na cewan hukuncin be yi ba duk da akwana na bakwai dinan akwai horo mai tsana ni da za su sha. da ga haka aka hasko fuskokin su wanda ruwan hawaye kawai suke yi, gaba ɗaya na cikin kotun aka hasko sanan Camera man ya fito waje yana hasko yadda ake sanya su cikin mota mutane sai za bura suke yi kaman zasu kashesu, dan ɗa gyar muta ne suka yadda na ukun yarasu sa ka makon harbinsa da akayi dan sun ce muta ne uku ne. Jita yi jiri na ɗibanta a haka ta suma, dan kanta ta farka bayan wani lokaci, a firgice ta yunƙura tsaye badan an kulle ta ba da sai fa fi ce daga gidan, kuka ta sha sosai sai can ta samu natsuwa tana kallon agogo wanda ke nuni da ƙarfe 5pm na yamma, toilet ta shiga ta sakar ma kanta shower ta na mai tunanin abin da ya janyo kusu wannan mugun ƘADDARA. END. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [6/28, 09:05] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Typing Page 27. Flash back Ita marainiya ce kahu ne ya tsinci ta tin tana jaririya, sai ya kaita rigarsu can ƙasan ƙauye malam auta, ko da ya kai yarinyar sai da suka samu saɓani da matarsa Adda wacce yaronta ɗaya mai suna Mus'ab, to da yake Adda na ta tausayi yasa ta yadda ta amsa jaririyan wacce ke ta tsala ihu, da madarar shanu suka raini yarinyan wacce suka raɗa mata Sakeenat, kahu mutum ne mai son karatu dan haka yasa rayansa makaranta, a haka kullum suke wahala gurin fitowa daga ƙauye zuwa makaranta dan sai an shiga cikin gari ake samun makarantar ma su kyau, a haka suke lallaɓawa har suka gama secondary sai ya sanya su makarantan koyan na'ura, da ya ke ita Sakeenat Allah ya bata fasaha sosai sai ake ta ma ta jumping daga low level har high harma ta wuce tabar yayan na ta, sannan a lokacin suka bar rigan suka dawo cikin gari suna rayuwa, ɗan Sakeenat ba makaranta kaɗai ba hatta wasu da ga wani guri sukan kawo mata aiki, kaman in ayi ma mutum hacking account ɗin sa, ko bank ta samu matsala ɓarayi to akan ne me ta ɗan warware cases ha ka, A wata ranan Jumma'a ranan da ita ce silan rugucewan komai na rayuwan su, mota ce me ɗauke da tambarin EVANT INTERNATIONAL SCHOOL a jiki bayan motan ta zo wucewa da matuƙar gudu, Adda wacce ta je byuɗe account a bank sai ta yi mantuwa passport dan hakan yasa ta miƙo hanya cikin sauri sauri, ta zo tsallake titin kenan wannan mota ta taho da mugun gudu, take suka yi ciki da ita, ganin ya kaɗe mutum yasa motan ta tsaya, gaba ɗaya student din suka fito, ganin mace kwace cikin jini, da yake safiya ce ba yalwan muta ne sosai, Driver din ne yasata cikin napep tare da bawa me napep din kuɗi daya kai ta asibiti, sanann ya koma motan tare da cika umarnin ƴan matan daya ɗauko, yaso ya kaita asibiti amma sun ishe wai yabarta gudun ƙar susa a koreshi a aiki yasa ya ta da motan, Me napep ya jaita wani asibitin gomnati sukuwa suka ce dole sai an fara biya kuɗin komai tare da ɗauko police saboda accident ne. Me napep anfani yayi da wayar majinyanciyan ya ƙira number ɗaya gani a farko an sa My SK. bugu biyu Sakeenat ta ɗauka, basu yi wani gausuwa ba ya faɗa mata komai a matuƙar rikice taje asibin tana isa suka hadu dashi me napep din, labarin komai ya bata yana sannan ya wuce, gurin Adda tanufa wacce ke kwance cikin jinin dan harsun bubbushe, haka Sakeenat ta dinga zage asibiti da Adda tana rogon wanda ze ceci ranta amma kowani Doctor ta samu sai su zulle, haka ta samu ta zauna tana kallon Adda, sai a lokacin ta kira Kahu da Mus'ab, cikin minti 30 sai gasu, su kansu yadda su ka ga Adda sun san babu rai ajinta, basu ɓata lokaci ba suka nufa gida da ita aka mata sutura sannan aka kaita zuwa ga makwancinta, Sakeenat ta sha kuka kaman ranta ze fita, ana kwana uku da rasuwan sai Sakeenat ta nufi makarantan, da ta je da ƙyar suka bari ta shiga ciki, head office ta fara zuwa, tana nan ta yi mai complain akan abin da ya kawato buɗan bakinsa sai yace "Ranta kike so mu dawo da shi ko mene? Malama nan kasuwanci muke yi za ki iya tafiya." Ba ta yi mamakin jin haka dan tafahimci tin shigorta irin kallon da yake mata. A daidai nan ƙararrawan makarantan ta kaaɗa in da ɗalubai mata suka dinga fitowa daga classis, dan mata ne zalla, musulmai da Chirstans ne amma dukkansu babu wanda ya sanya Hijab ɗaiɗai ne masu hula. tafiya ta farayi tana mai kallon makarantan dan ya matuƙar burgeta, ko da takusa fita sai ta hangi school bus guda 5 a parking lot, sai ta nufi gurin tana zuwa tayi ma ɗan tsohon da ta gani magan bayan ta gaida shi ya amsa "Sir pls ƙasan drivers din motocin nan?" " Eh Madam nima ɗaya daga ciki ne, lafiya?." " Eh lafiya, akwai wanda ya kaɗe wata mata 3dys back, shi na ke ne ma." take jikinsa ya yi sanyi tare da dabur ce wa " Ni....ne me yafaru." kalman 'nine' sai da ta ji wani irin a hukunta take ta kulle idanuwan ta sannan ta buɗe duk sun sauya launi, zama ta yi gyefansa da taga wani kujera. " Kai ne ka kashe min Mama, sannan katafi kabarta a gurin, naje asibiti na dinga yawo da ita sunƙi amsa ta harta mutu, ba wai kuɗi ne ban da ba amma sunƙi ma amsan ta gaba ɗaya." ta kai magana tana share kwalla, shima kuka ya fara yi yana tsugunnawa har ƙasa yana mai ce wa " Wlh ba da sona ba ne, ki ya femin ina cikin motan yaran ciki sun sani gudu, ga complain da suke tamun banyi au ne ba na kaɗeta, na so na kaita Asibiti amma yaran suka ce abakin aikina shine na ba da kuɗi don a kaita." " Bangane ba? suwaye yaran ?" Ta jero mai tambayan bayan ta ɗaga shi daga tsugun nan. " Eh student's ne amma wani ban zan tsari ake dashi ba'a tankwarasu, harda teacher's ni kai na badan banda wani sana'ar ba ta tuni na bar makarantan." " Hmmmmmm yara ne su?" " A'a sun ta sa teenagers ne." " Zan kai ƙara koto dan haka sai ku jira sammaci" ta miƙe tsaye daidai nan P.C ya iso gurin yana mai ce wa " Kotu, kotu kika ce, to Allah ya kaiki lafiya, masu gadi ku min waje da ita" haka yasa masu gadi suka koreta da cewa kar su kara bari ta shigo. Samun guri ta yi ta zauna tana kuka sai bayan da ta gama sannan ta wuce, a hanya ta ga station ba dan ta shirya ba ta shiga ciki, gaishe da wani ta yi sannan ya ta zauna gurin wani ta wanda ta faɗa mai komai, amma dajin sunan makarantan ya ce ta yi haƙuru makarantan na Babban Barrister ne, kuma makarantar masu kuɗi ne faɗa da su babu riba, duk hanyar da tabi sai tozarci da hulaƙanci, haka ta koma gida jikinta babu ƙwari, zama tayi kusa da Mus'ab tana mai ce wa " Yanzu shike nan wa'inda suka aikata sun sha, dukda yara ne amma ai sun san rai dai." " Ki ya ƙuri kinji mubar maganan." hawaye ne yaci gaba da sauka akan fuskanta, jin abin da ya ke faɗa, take hankalinsu ya koma kan TV dan jin Rash ne yauma ya sheƙe wasu, take brain ɗin ta ta hasko mata abu a ciki, sai tasaki murmushi tana kallon Mus'ab, shima da mamaki ya ke kallon na ta sai tace " Na sa mu Idea akan abin da zan aikata akan wancan makarantar." " Me ke nan SK?." take ta faɗa mai yadda brain dinta ya mata huɗuba, sai yaƙi yadda saboda tsoro amma sai da ta samu ta shanyo kansa, haka Kahu shima, aikuwa washe gari ta koma makaranta, sun hata shiga amma sai da ta haɗu da tsohon nan, bayan sun gaisa ya ce da ita " Ƴata ni yanzu na ma fara azumin kaffara, ki ya ƙuri banda kuɗin da zan biya diyya." " Ni ba dhi ya kawo ni ba, na kai case din kotu kuma sun amsa sai dai na yi wani tinani kawai abu ɗaya nake so in kamin shike nan komai ya wuce." har jikinsa ya fara rawa, cikin karkarwan murya ya ce " Ina...jin..ki." sai da ta yi murmushi sannan ta ce " Sunayen yaran dake cikin motan kawai nake so tare da numbers dinsu, zan bi gida gida gurin iyayensu." "Ranan su 30 ne kawai sai dai Madam yaran ba suda tarbiyya, a ganina iyayen ma basu dashi." "Karka damu." daga haka ya koma makarantan, cikin minti 20mnt ya dawo tare da ba ta takadda, " Da ya ke akai file dinsu shine na kwafa miki, Nagode Nagode." " Ni ce da godiya, dukkan su suna da wayoyi koh?." " Eh Madam manya manya ma kuwa." sallama suka yi ta koma gida abinta. Bayan isha'i ta zauna da system dinta tare da bincike akan ko wani number anane tafahimci gaba ɗayansu yaran masu kuɗi ne sosai, ko da taje gidan wasu daga cikin sai hulaƙanci da cewa ai Driver din za tabi ba yaran su ba, hakan yasa ta shirya babban plan akansu, wanda cikin fasaha da kwarewa ta yi shi. A yau Laraba shine ranan da ta zaɓa. Zaune ta ke a cikin wani hole in da ya ƙawatu dan ta kashe kuɗi sosai, ƙarfe 11:30pm dai dai, yara students suka fara shigowa ciki, nan danan suka haɗu a cikin gurin in da ya ƙawatu ga kuma abubuwan sha iri iri aikam suka sha dan wanda ke bakin get din gurin ya ce har Zee ta zo amma ta je ta dawo, can sai ga Zee Ita ma ta zo aikuwa gurin ya hau shagali kaman me, suna rawa jiri-jiri na ɗiban su a haka duk suka zuɓe agurin, fitowa SK ta yi tare da Mus'ab sai Kahu, nan take suka kwashe dukka yaran suka sanya su cikin babban mota, sai wani ɓoyayen gida wanda ba'a gama ginawa ba, anan suka yi komai harda video akan Garkuwa da Rash ya yi sannan suka watsa a duniya, suku ma yaran da suka farka kowa ya bada number babansu, a take sa ƙo ya shiga akan gobe ake da ɓugata tw Million akan kowa, sun san kuɗin be yi yawa ba duba da iyayensu na su masu kuɗi ne sosai. Ko da washegari ta yi duk SK ce ta haɗa komai, tare da ɓoye sunan account din da suke sa kuɗin, tayi wasa da hankalin muta ne sosai, dan in dai na'urace dole a sara mata. sannan kuɗin ko da suka shiga direct gidan marayu suke zuwa da wasu ma ta sa ƙarfi, na ƙauyuka, da gidan talawaka sai dai su yi ta ganin ɓoyayyen alart na maƙudan kuɗaɗen. Sai gashi anyi ram da su, amma ta san akwai wani, wani can wanda ke bibiyan na ta, wani mayen na'ura, shine ya yi mata tarko kuma ta faɗa dan ƴan sanda ta wuce hasashen su da tinanin su. END. 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊 [6/28, 20:59] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 28. Continuous Wankan ta gama sannan ta fito daga bayin gurin kayansa ta buɗe, wando da riga ta ɗauka ta za ɓa wanda zai yi mata ta sanya sannan ta koma Parlour tana mai bin ɗakin da Idanuwa, sai ta koma gurin window tana hangen compound din gidan iya in da take iya hange, mamaki ne ya kamata amma sai ta share ta koma Parlour ta yi zamanta tana mai ƙurama wani guri ido ko ƙaftawa bata yi, sai misalin 7pm na yamma ta jiyo jiniya na motoci, sai ta koma tana leƙe, a ranta tana cewa 'wai dama nan gidan Governor Aliyu Haidar abdulqadir ƙanƙara ne, wow'. Jami'ai ne ta gani sun kewaye gidan, shi kuma shugaban gayyan ya shige ciki tare da matarsa wacce ta sanya kayan police, jita yi an cire key ɗin ƙofan, ta ma san wane ne, me dakin ne ya iso, aikam yana shigowa ya kulle ƙanshin tirarensa taji ya doke ta kaman ba tin a station ya shirya ba, karaf idanuwan su suka haɗu guri guda, take zuciyarsa ya tsinke, a hankali ya furta " Na same ki lafiya?." Kai kawai ta ɗaga mai, sai ya shige bedroom, yana shiga ta fito ta dawo ta zauna a kan kujera ta na ta tunani kan taya zata samu na'urori dan na ta duk yana wajen ASP wanda ba ta san sunan sa ba, sai bayan ya yi wanka ya fito, shima zama ya yi, sai ta zame zuwa ƙasa tana ce wa "ASP wani aiki zan ma ka sallame ni da wuri dare ya nayi." "Babu in sa za kije ai." ya faɗa da kakkausar muryansa mai daɗin gaske. jitai kaman ba ta ba ta fahimci abin da yace ba, sai taji ya ci gaba da ce wa "Ina da wani surprise da zan minki yau." haɗe fuska ta yi sosai, ranta in ya yi dubu ya ɓaci ace ƴan uwanta an kamasu amma yana ce mata akwai surprise da ze mata, gani take komai na duniyan sun isheta dan ma ta na da karfi hali, ya dai taimaketa dan haka ta ayyana ba ra dai ta ga iya gudun ruwa shi dai, Nan take yaji an fara Knowcking kafin ya ce komai aka buɗo aka shigo dan ne sa key ba, da idanunta ta bi su cikin mamakin da ya cinyeta, sai da ta iso tsakiyar Parlourn ta buɗa baki ta na ce wa "Yaya Umar, me wannan matsiyaciyar take yi anan? harda sanya kawayanka? Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un." Be ba ya amsa ba, domin be ma san me ze ce mata ba, yasan be kyauta ba daya barta a cikin ɗakinsa kuma su biyu amma be ka mata Fatima ta furta haka ba, be ka mata tayi mai mugun zargi ba, Idanuwan sa ya lumshe sai ya buɗe da sauri dan jin ƙaran mari Tas, ya za ci Fatima ce ta mari Sakeenat sai ya ga saɓanin abin da yake tinani, Sakeenat ce ta dallama Fancy mari, idanuwanta ta ƙara waresu, sannan ya ga tana naɗe hannun rigarta tana ce wa " Maimaita naji, wace ce matsiyaciyar? Ki kiyaye harshen ki ko na murɗe muki wiya, ba'a zagina a kwana lafiya." Takai maganan tana tsayawa gabanta wanda sun haɗe, sun haɗa kafaɗa, sai dai Sakeenat doguwar ce dan ta bi Fancy tsayi, itako Fancy marin ya shige ta sosai, ga hawaye da suka cika idon na ta, ta so Zaki ya yi magana amma ya yi tsit hakan yasa ta yi ƙwafa da ƙarfi ta fice da cikin gudu-gudu... *************** ********************* Tin bayan wayan da suka yi cikin daren jiya, ta ƙudurta washegari za taje don ganin ƙawarta don ta ce mata tana son ta zo suyi wani sirri, bayan ta kammala aiki har abincin rana sannan ta shirya ta yima Maman Rabi sallama ta ɗauko hanyan milinium city, ba ita ta isa ba sai ƙarfe 1:12pm, tana shiga sai data yi sallah sannan suka hau hiran yaushe gamo, kaman ba kullum suna tare a waya ba, jin yau za'a tsai da ranan auranta ta re ta biyan sadaki yasa ta yanke ce wa anan za ta kwana kawai sannan taje ta nemi mara kunyan da ta faɗa mata ɓakan magana a waya jiya. tare suka ci abinci a daining area, hira suka sha sosai a yinin ranan, Ramlat tayi-tayi takwarar ta faɗa mata maganan da za suyi na sirri sai tace ta bari washegari kawai. tin jiya rabon da suyi waya da Zaki, sai misalin 6pm ya kira bayan sun gaisa ya ce ma ta " Yanzu Pazars sun ƙira ni akan an tsaida 3 mounth, har sa da ki sun biya naji daɗin yadda suka ce an karramasu na gode Babyna" sai da ta yi murmushi sannan ta ce "Allah sarki ba damuwa, Allah ya nuna mana, Ni ma ai nice da godiya." " Hmmm na so zuwa yau amma gobe zan zo, tare da surprise da zan miki." " In ka so kagan ni yau za ka ganni dan a gidan ku zan kwana, in ka samu time ka leƙo kawai Part ɗin Babban yaya." " Wow ma sha Allah, ki ce kin zo gurin matar Boss kenan." " Uhmmm " Daga haka suka ra bu, amma bayan minti 30 sai ya kuma ya kiranta tare da ca mata, dan Allah an jima ze kira ta sai suzo da matar Boss ya nuna mata surprise ɗin, da harta mu sa amma sai ta amince tinda su biyu ya ce suzo kuma ya ce baze iya zuwa da surprise din ba ne. suna idar da Isha'i suka sha hijabai sannan suka fita bayan Ramlat (Kifaty) ta sanar ma Babban yaya ta waya kuma ya yadda. sannan suka fita ta ainiyin ƙofa fyuta suka fara tafiya suna hira, guards sai gaishe su suke yi, compound din abin sha'awa duk da dare ne amma gurin aikwai watan haske sosai ga muta ne ba laifi, sai dai suka sha za gaye da ƙafafun su, suna hira abinsu gwanin sha'awa dan ƙawance su ya koma ƴan uwan ta ka. End ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿. [6/29, 19:26] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Page 29 ****************** ***************** Ta na fita sai Sakeenat ta juyo ta na ce wa " Wace ce wannan yarinyar? shi ya sa nake ta ce mata ka sallame ni ina son na tafi, akwai abubuwan da nake so na yi gaskiya." Be tanka ta ba ya ci gaba da kallon TV abinsa sai da ta kuma magana shine ya jiyo ya kalleta kallo irin na ƙurulla " Ko ka bar ni na fita ko kuwa na fice da kaina, na iya gudu, fita cikin gidan nan ba ze bani wahala ba, sannan katangar ƙarama ce tsab zan tsallake ta be da wani tsayi, duk da akwai jami'a daya wa amma tsab zan fece." " Hmmmm da gaske." "Kwarai kuwa, na kwada maka ne?" Ta faɗa tana ɗaga girarta ta da ma. "A'a bana so, na san za ki aika kin san ke WANTED ne, kuma am ba za hoton ki a ko ina." "In dai wannan ne karka da mu zan sauya shiga ta da yadda na ke, and faɗa min me ya sa Camera ya yi yawa a gidan nan, gurin shigowa iya wanda na gani sun kai 15, sannan Parlour din nan akwai, duk saboda Gomna ne?" cikin rashin fahimta ya ce "Cameras kuma!? Ban san waye ya sanya su ba, amma ya aka yi ki ka ga ne su?." " Hmmmmm ba ka san wace ce SK ba akwai kwanya." " Mayyuwa saboda tsaro aka sanya su." " Haka ne amma har a cikin ɗaki abu mara daɗi ma, masu record ne da kansu kuma ko da yaushe suna aiki sai dai ban san ko me anfani da sola ba ne ko na nepa ne." "Yanzu bara dai na je masallaci ina zuwa." ya miƙe yana mai nufan ƙofan ya fita, aikam yana fita ya murza keys, murmushi ta sake sananan ta shiga bedroom hijab din da matan ɗa zu suka ba ta, shi ta sanya ta yi sallan a wajen ta zauna har taji shigowan shi, amma ba ta motsa ba, shima ko da ya shigo zaman shi ya yi a Parlour yana mai tinanin yadda ze ceci ƴan uwanta. Knocking ya ji yasan su Ramlat ne dan ha ka ya ce " Bisimillah." aikam suka buɗe suka shigo bakin su ɗauke da sallama, ya amsa yana mai sakin fuska sosai, sanann ya gaida matar Boss aikam ta amsa, zama suka yi sai Babynsa ta fara magana "Wai mafin ka zo da kan ka kai shine ka sa mu zo, toh gamu ai, mene ne surprise din." Har ran shi yana son Ramlat sosai komai na ta na burge shi yake sai dai akwai wani yanayi dabam da ya keji akan waccan Sakeenat din wanda komai na su iri ɗaya ne harta muryansu abun ya bashi matuƙar mamaki, sai dai in ya tuna waye ALLAH da girmansa sai dai yace 'ma sha allah'. "Gajen haƙuri, surprise din yanzu zan nu na muku." kafin su yi wata magana sai ya miƙa ya nufa Bedroom, Kifaty ita dai kallon TV take abinta, amma Babynsa da idanu ta rakasa tana mai godiya da Allah ya bata wannan amatsayin saurayi kuma nan da ɗan lokacin za su yi aure, Zaki mutum ne kyakkyawa mai duhun launi, mai faɗin ƙirji ga tsayi, tafiyarsa ma abin kallo ce. Gani take duk duniyan nan Zaki yafi kowa a wajen ta, gashi da addinin ga ilimin boko, sannan ya iya za ma da muta ne abu mai jan hankali ma shine akan aikinsa akwai riƙo da gaskiya. Sai da ya shiga ta bar kallon gurin, ita ma ta mai da Idonta ga TV. Yana shiga ya hangeta zaune ta na tasbeehi, tana ganinsa sai ta shafa addu'an ta miƙe tare da cire hijab ɗin ta kallon sa ta yi tana mai ce wa "Dare na yi ina son na wuce gaskiya, sannan ina neman wani taimakon ka guda ɗaya kawai." " Faɗin kan ki tsaye." " System nake so, kun kwashe min kayayyakin aikina wanda ƙoƙarina da hazaƙa ta na ciwosu." "Kayan ki sunanan na a dana miki domin da su za ki yin aikin da zan saki." idanuwa ta ware tana mai jin daɗi sannan ta ce " Na gode sosai bawan Allah, idan ka ba ni da su zanyi anfani na ce to su Kahu." " Da gaske?." "Eh mana." "To yanzu dai mu je na nuna miki surprise din, na san tunda aka haife ki baki taɓa ganin wannan surprise din ba." ta ɓe baki ta yi sannan ta taƙo gabansa wanda duk taku ɗaya yana ji har ran shi, a gabansa ta tsaya sannan ta ce "kafin nan faɗamin aikin?." "Secret ne, ban san ko wa ya san ke ce mayyan na'urace, kullum daga 9am zuwa 5pm, za ki dinga zuwa gurin da zan miki kwatan ce." " An gama tin da ka ce ci raina komai zan ma ka." "Mu je." Daga haka ya fita ita ma ta bishi, ko da suka isa Parlour din, sai ya yi ma Ramlat nuni da ta ɓoye a bayansa fuskanta a haɗe dan ita ba ma'abociyar son wasa ɓa ce, ta na da dariya amma ba a gani sam saboda ɗauke fuska. END. 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊 [6/29, 19:27] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/lqfbwo1tifs84zut6x2xs9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rs40ab7s9ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄ƙ𝐈 ďăğă ăĺƙăĺăмĩм рŕĕťťŷ śķ page 30. " bismillah ga surprise din...." a tare suka wai go ramlat da ramlat din, shi dai sun ga mace wacce ta ɓoye a bayansa, dan ta juya fuskan ta ne. " lafiya ta ɓoye? ohhhh ita ce surprise din wai?." sai ya ɗaga ma babynsa kai alaman eh, sai ya matsa gefe guda take fuskokin su suka yi arba da juna, ita kanta kiyaty sai da ta ɗan razana, tsakanin sakeenat da baby ramlat an rasa wayafi shiga firgici take ramlat ta zuɓe ƙasa sumamma, sakeenat kuwa kanta ta dafa a matuƙar tsora ce jitai kaman ta kurma ihu, mace tagani sak ita, tsayi, jiki, skin colour, murya, abin da ya banbanta su shine kayan jikinsu sai kuma ta lura ta fita tsoro, a lokacin ramlat ta farka bayan ta kwararta ta yayyafa mata ruwa, tana buɗe idanu sai suka ƙara haɗa ido guri ɗaya da sakeenat, a tare suka yi kan juna suka rungume dan ƙarin tabbatar wa, mamaki da almara sun cika su, sai bayan 10mnt aka samu su ka natsu, zaki har ran shi yana tinanin ko dai tweens ne, labarin juna suka ba juna, kowa kallon photocopyn sa kawai yake. " dan allah matar boss, ta kwana a wajenki zuwa gobe za ta wu ce." " ayya babu damuwa." daga haka suka yi sallama suka wuce, taso su shiga main parlour amma ta ce su huce kawai, suna shiga ɗakin ta ramlat ta sauka nan ita ma ta kaita, da ƙyar suka iya cin abincin daren, haka dai ta barsu ta koma na ta ɗakin tare da ɗaukan wayanta ta kira boss, kiran na katsewa sai ga na shi ya shigo, sai da ya kusa katse ta ɗauka tare da yi mai sallama, ya ko amsa, " honey ba ka dawo ba dare na yi fa, kana ina yanzu?." " kifaty ku kulle ko ina, sai gobe zan dawo, naje ganin doctor ne, mun haɗu amma akwai abin da zemin ne shiyasa in kuna kina so na dawo cikin dare toh." " a'a goben ka dawo." sai da ya sassauta murya saboda har na ta muryan ya kashe mai jiki " kisan mene ne?" " a'a honey sai ka faɗa." "alhamdulillah yanzu na sa mu lafiya sai ki shirya zuwa gobe dan na kai ƙarshe, zan ta wo da kazar amarci." shuru ta yi ba tace komai ba, ta ji daɗin samun lafiyansa amma ba ta shirya gobe ba sam ba ta shirya ba. " shike nan mu kwana lafiya." " har za ki kwanta." "eh" " make sure ki kulle ko ina, please." dayga haka ta kashe wayan, kallon time ta yi ta ga 10:00pm sai ta shiga contact ta lalubo meerah wanda tin tini suka yi exchanging number, kira ta yi aikuwa bugu biyu ta ɗauka da sallama sai ta mai da mata sallaman "fatan ban tashe ki ba koh?." " haba ina ni ina barci tin yanzu, ai sai anjima ko dan akwai abubuwan da zanyi, lafiya dai koh?." "eh lafiya amma ƴar taimako nake so kimin kinji kuma sirri ne fatan ke kaɗai ce?." take ta ɗago daga cinyan aliyu wanda da ɗaura kanta, ta shiga bedroom sannan ta ce " eh toh na matsa yanzu, inajin ki." " pls sis takwara magani nake so ki taimakamin da shi." " magani ? me ke damunki?." " ba komai ba ra na raɗa mi ki." nan fa tayi kuskura wanda meerah ce kawai ta iya ji me ta ce, sai meerah ta yi murmushi ta na ce wa "wai dama shine kawai, karki damu ina da su kala kala, yanzu dai yamata tin yau kifara shansu, na aiko miki guard ne kawai." "a'a sis ba ra mu zo da ƙawata amma ta ƙofan main parlour zan shigo." daga haka suka yi sallama, sai ramlat ta miƙe ta nufi ɗakin baƙi, samun su ta yi suna hira, sai ta ce "ramlat plsssssss sa ƙo zabki rakani na amso gurin meerah ta main parlour" " okh." tabko zura hijab dinta dan dama ne man haɗuwa take da fatima ta gasa mata magana, sakeenat sai ta miƙe tana mai ce wa " muje tare sis, aunty babba ki zauna kawaim" kamar ta ce a'a sai ta barsu, ta main parlour suka bi wanda babu kowa sai tv dake aiki, ita dai sakeenat abun sun ba ta mamaki ace ko ina cameras, suka zo daidai ƙafan meerah sai ramlat ta ce " sk zanje wancan ɗakin, ki shiga ki amso saƙon sai ki jirani anan." kafin sakeenat ta ɗaga mata kai, ramlat kuma ta nufi ɗakin su fancy. knowking tayi sai aka ce 'shigo' hakan yasa tashiga kanta tsaye, tanata lura da gidan da abubuwan da ke cikin gidan, duk da gidan gomna ne amma securitys din sunyi yawa, babu kowa a tanƙamemen parlour wanda ya ƙawatu sosai, sai can wata tafito sanye da dogon hijab, a kallo ɗaya ta gane police din can ce , abu ta ba ta sai ta amsa, sai tamata sai da safe sannan ta fice. tsayawa tayi a inda ramlat tace har ta ga ta fito tana murmushi, tare suka jera ba dan sakeenat tasan meyasa ramlat din ke murmushi ba. ko da isansu part din boss, kifaty na kallonsu ta ce " takwara kinje ɗakin su fancy ko?." " na je amma ba gunta naje ba, gurin baby naje." ta faɗa tana za ma sannan ta ci gaba da ce wa "kema kinsan ni, naje nayi mata baƙaƙen maganganu ne da za su hanata barci." " allah ya shiryeki dai." sakeenat dai shuru ta yi tana buga lissafi a cikin kanta. a ɗaki ɗaya suka kwanta. end. ďăğă ăĺƙăĺăмĩм рŕĕťťŷ śķ ✿◡‿◡✿ [sakina abdullahi] ✿◡‿◡✿. [6/30, 09:17] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Page 31. **************** **************** Da sauri-sauri gudu-gudu ta haɗa tana shiga part dinsu tana mai zub da hawaye, ba ban Aunty ta ce ta je ta kira Zaki ba, da ba za ta sake zuwa part din shi ba, Aunty ce kawai a parlour sam ba ta lura da yadda ta shigo ba har sai da Fancy ta bige wani flawer class har ya fashe, sai ta shige part din su, da mamaki a fuskan Aunty tana mai tinanin lafiya kuwa dan wayan Zaki baya shiga ne da sunyi waya amma ta na fatan ba wani abu ya yi mata ba, ta na shiga guri guda ta samu ta zauna tana kuka mai sauti, gaba ɗayan su suka kewaye ta suna son jin ba'asin me ke damunta amma ta kasa magana dan kuka yaci ƙarfin ta, sunyi sunyi amma taƙi magana, dan haka suka barta dan ta wuce. Sai bayan kaman kusan hour sai aka musu knocking sannan Baby ta ba da izinin a shigo, tana buɗo ƙofan suka hada ido da Kandy take fuskanta ta sauya, shiga ta yi da Baby da Tweens ne kawai suka gaisa, sai Hasty ta ce " Ƴar uwa shine sai yanzu kika leƙo mu, Tom ki kwana anan ma na." "Ayya karki damu a can zan kwanta kinji." " Please da kin kwanta ana ......" " Ba mu da masaukin wannan ƴar iska anan ɗakin." Tin bayan shigowar ta ba ta furta komai ba sai yanzu, ta faɗa tana nufo Ramlat, ita kam Ramlat din jin daɗi ta yi dan an zo in da ya da ce. " Hmmmm ke ƙaramar mara kunya ce, faɗamin arziƙin da ke cikin gidan nan na ki n ko na babank......" " Wallahi idan ki ka zagan mana Pazars sai munci mutun cinki anan." " Beauty bar ɓaƙar ƴar iska mana." ji tayi Ramlat ta wanke ta da mari sannan Beasty ita ma ta tsinka mata mari, take Kandy ta yo kanta a fusa ce nan ma ta wanke ta da mari sannan ta ce " Wallahi ban ga me ta ɓani a cikin ku ba, ku fita a idona na rufe wallahi." " Sisters ku gyaleta kun sani rainon talauci sai haƙuri." Faɗin Karis tana daga zaune abinta, har Ramlat ta juya za ta fita sai ta dawo ta matsa kusa da Fancy ta raɗa mata abu akunne sannan ta fice tana murmushi. *************** ****************** ko da safiya ta yi misalin 9am tara na safe, Sakeenat ta shirya bayan ta ara kayan Kifaty ta sanya, sanyawa ta yi da yake dogon riga ce kuma yama Kifaty ɗan tsayi sai Sakeenat ta shanye ta, a tsaye ta yi breakfast sannan ta fice, bayan ta ce ma Ramlat za ta je har gida dan taga gidansu kuma su ƙalla ƙawan ce, dukkansu sunajin har ransu suna da dangan taka a tsakanin su. Direct cikin wajen ta shiga in da ya yi mata kwatan ce, ta na shiga ta hangesa zauna cikin manyan kaya wanda haibarsa da kamala sun bayyana mai sosai, gaisuwa suka fa ra sanann ta ce " Kasan menene?." " Sai kin fa ɗa." "Akwai wanda ke bibiyan familyn ku agani na." sai da ya gyara zama sannan ya ce "Kamarya?." Miƙa mai ƙananun Camera ta yi ta ce " Ga ka irin wa'innan sunfi 100 a gidanku, ina ji akwai me sa ido akan ku." "Za mu yi wannan magana daga ba ya, yanzu zauna kifara aikin na ki." zama ta yi kan kujera sanann ya miƙa mata jakka wanda abubuwan ta ne a ciki, tana gani ta hau daɗin murna harda pi to. "Na gode sosai Zaki, yanzu dai ina son sanin location ɗin da aka kaisu kahu." Take ya ciro wayansa da karanto mata, nan da shiga operating cikin matuƙar kwarewar daya ba Zaki mamaki, cikin ƙanƙanin lokaci ta nemo station din da kaisu amma abun da ya matuƙar ba ta mamaki shine wani babban al'amari ta gani wanda yasa zuciyarsa tsayawa cak. END. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [6/30, 09:25] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Part 32. ************* *************** Tun jiya ranta ke ɓa ce, saboda kalaman da Ramlat ta yi mata a kunnuwa, a haka dai suka shirya dan zuwa makaranta, ko da suka fito Parlour sai da Mom ta tambaye ta " Fateema me ke damunki?." " Kaina ke ɗan ciwo." tana faɗin haka ya sa dukka su huɗu iyyaye matan na su suka zuba mata ido, ta so zuwa school amma Aunty ta ha na ta tare da ba ta magani ta sha ta kwanta, ba ita ta tashi ba sai 11am, ta yi wanka tare da fitowa, a lokacin walwala ta ɗan dawo, za ma ta yi tana kallo sai wayanta wanda ke Ringing ganin number ne ya sa taƙi ɗauka saboda umarnin Babban yaya, amma da ta ga an kira sau 6 yasa ta ɗaga tare da sallama, amsawa tayi badan tawayi muryan namijin ba. "Nasan baki gane ni ba, ni ne Sir Muhammad Anas, M.D." yana faɗin haka ya sa ta waro ido, dan daga faɗan sunan na sa ta gano muryan sa, malamin English ne, wanda gaba ɗaya makarantan su suke ji da shi, gaye ɗan wanka, matashin mai ƙananan age, ko wacce mace so take taga ya kulata dan ko magana ya miki ranan ji za ki yi kaman an miki bushara da gidan aljanna. " Na gane, Good morning Sir M.D" " Morning beautiful how was your day." " Alhamdulillah." " Ma sha Allah ban ganki a school ba, hope everythings is 5ne?." ƙirjinta har dukan uku uku yake yi, wai Sir M.D ne ya kira ta, sai da ta kwantar da murya sannan ta ce " I feel headache." " Ya Allah. Sorry wishing you quick recovery beautiful." " Thank you Sir." " Don't worry, excuse me , I will call you letters." kafin ta ce komai ya katse kiran, da idanu ta bi wayan tana mai mamaki sosai, wai Sir M.D shine ya kirata, "Fatan ba wani abu na yi ba, Maybe na samu carryover ne a English?." Ta tambaya kanta ganin babu mai ba ta amsa yasa ta koma ɗakinsu. Tana tuna kalaman Ramlat "Gaskiya ajin ki ya zuɓe anan, kuɗinki ya siya miki soyayyan My Asad, please adinga ka ma kai dai." *************** **************** Hannu ya sa ya rigo na ta hannu ganin ta yi baya kaman zata faɗin, ya riƙota amma firgici data shiga sai dai mumfashinta ya ɗauke hakan yasa ya janyota jikinsa, be wani tsaya yi mata wani abuba saboda shima yaɗan tsorata da yanayin na ta, direct yasa aka shiga da ita asibitin da ke kusa da station din, alluran barci yasa aka mata don ta samu natsuwa. komawa ya yi in da ya fito ya tattara ta kaddun gun tare da ƙara kallon abin da ya janyo mata wannan razanan, system din ne kunne wanda yake nuna wani babban guri na ci da huta, in da suka tabbatar station din da aka sanya su Kahu ne. ****************** **************** "Labarai da ɗumi ɗumin sa, a yanzu rahota ya iso ma na, na cewa Staion ɗin (Right and peace) wanda ke burnin Abuja, Unguwan Sultan Hakimin ƙaramar hukuma, wannan station din wasu matasa ɓa ta gari sunyi daran mikiya sun cinna mai huta in da ya janzo mutuwan wannan masheƙin me suna RASH da ɗan uwansa wanda a yau ake so amiƙasu a kurkukun dake Kazaure, sannan da wasu wa'inda suke kulle, jami'an 5 suma sun ƙone da wasu iyali wanda shigansu kenan ciki dan an kama yaransu a daren jiya." matashin saurayin wande ke zaune yana zu ba rahoto a cikin majigin TV, take kuma aka saki faifan Video din yadda wajan ke ci da huta, hannu yasa ya ɗauki remote din TV ya kashe, furzar da iska ya yi yana mai jin babu daɗi akan abin da ya faru, family guda basu ba basu gani ba, daga ƙaramin kuskure sun halaka. *************** **************** "Gobe sai ku sa ki saɓon Video din." ya faɗa da muryansa mai amo da cika kunne, sai Adamsi ya ce " To RASH, amma aganina karmu saken video, tin da yanzu duniya ta san RASH ya mutu, mubar shi a ya mutu kawai sannan Boss........" "Kuyi yadda na ce kawai, nan da kwana kaɗan salon aikin ze canza, sai na tan kaɗe ɓata garin tasssss." abin da ya faɗa kenan yana mai cire rigan jikinsa wanda gaba ɗaya ya canza kaman ba Shuraim ba, a murɗe yake ma sha Allah, rigan da ya zo da shi ya sanya a jikinsa sannan ya hau Wheelchair dinsa sai ya koma sak Shuraim, mota suka shiga suka bar wannan gida na sirrin wanda komai anan suke yi in dai abu ne a Kaduna, sannan kowa ni state suna da secret home wanda suke aikata ta'addanci na su a zahiri. ********** ************* ********* "Garin ya ya hakan ta faru? sam banjin daɗin haka ba." cikin damuwa ya furta hakan, sai ya yi jim bayan wani sec ya kuma ce wa "shike nan Allah ya sa mu da ce." sanann ya katse wayan, tinani yake yi idan duniya tasan ba wanda aka kashe ba ne RASH, ya so RASH ya bayyana kafin ranan da'aza hukunta su Mus'ab amma gashi an ƙona gurin harda wasu bayin Allah, ya san manyan muta ne ne suka sa ayi wannan aika aikan, dan shigowar shi kenan wannan baƙin labarin ya riske shi, ko da ya dinga canza channel duk dai zan can kennan, kuma abin haushin shine yadda muta ne suka fito suna nuna farin cikinsu akan mutuwar RASH, tsaki ya ja mai sauti har sai ta sactary dinsa ya ɗago ya kalli ogan na sa. " Sun gama kammaluwa ne?." " Yes sir, duk sun iso." " Ok Ina zuwa." take sactary ya juya ya fice, sai da Aliyu ya ɗauki dan lokaci kafin nan ya fito, direct meeting section ya nufa ya shiga da sallama, ɗaiɗai kune suka amma, be damuba saboda yasa da halin ƴan jam'iyar ta su, zama ya yi a kujeran da yafi kowanne kuma ɗan me matsayi irin na sa aka ta na da, zama ya yi sannan ya kallesu tare da gaisuwar jumla, babu wanda ya amsa sai Samuel John, duk da shi chirstan ne amma ya fimai wasu musulman. Tattauna suka farayi kowa yana to fa albarkacin bakinsa gurin mus guna ma Aliyu akan aiyukan da yake yi be mu sa ba, sai bayan da kowa ya gama faɗan ma sa ra'ayin sannan ya ya ɗago idanuwan sa da suka ka ɗa suka sauya kala, sannan ya kalli wanda ke gefan damansa ya ce " List din da na baka, zuwa nan da yammacin yau ya bazu ya shiga tsarin dokon garin nan." ta ke musu ya kaure a cikin su, shikam ko a jikinsa ya fice, duk cikin mutanen gurin babu wanda yafi shaƙa kaman Shugaban kula da lafiyan al'umma domin yawancin dokokin ya taɓa ɓangarensa, a tare Pazar R da Pazar M suka fita suka bar meeting room ɗin. Office dinsa ya koma ya zauna yana mai tinani iri iri a ransa abubuwa da yawa sam ba su yi ba, sannan duk wannan lokacin ya yi shiru ne saboda ya gama fahimtar komai da komai. Zuwa yanzu kuwa ya fahimci komai dan yau ze fara gudanar da hukuncin da ko da kuwa be ma kowa daɗi ba. END. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [7/1, 06:20] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ Part 33. ***************** ****************** Bayan lokaci mai tsayi, abu zuwa uku sun faru, ciki kuwa akwai samun natsuwan Sakeenat dan zuwa yanzu ta falwala ma Allah tare da ɗaukan dangana, a wani gida take zaune wanda yake kusa da invda take aiki a ce wanta ba za ta koma gidan su ba, gidan su biyu ne kawai daga ita sai ɗakin ma su gidan, sannan ta ziyar ci gidan su Ramlat har sun gaisa da Maman Rabi ta so su haɗu da Babanta amma ranan ba ya gida, sannan zuwa yanzu bincike take yi sosai akan RASH ɗan yanzu ji take idan ba ta yi sanadiyyan kama shi ba ruhinta ba ze samu salama ba. Sai ɓangaren Aliyu Haidar wanda abin da ya zo da shi sa bo ne kuma tsari me kyau, in da ya umarci bincike akan duk makarantun da suke na private da a karya farashin kuɗin school fees, haka kan abinci komai sai da ya yi ragi a kai, sannan akan titina shima ya magance matsalolin da yawa idan mutum kuma ya ƙetara hanyar da ba nashi ba sai ya biya ta ra mai tsoka. sai makarantun government ya sa aka sauya mu su malaman harta asibiti duk sai dai ya yi bincike akan yadda ake kula da muta ne, idan ya ga abin da be da ce ba cikin ɗan lokacin ya ke gyara gurin, duk da hakan ya ja mai baƙin jinin gun wasu sannan farin jinin a gun talakawa. *************** ************** Air Force Base Kowa ya san dokan da ke cikin wannan unguwa, duk mutumin da ze shiga cikin unguwan dole sai an binciki waye, sannan idan kai baƙo ne dole wani na cikin Base din shi ze Kira ya sanar da amincewan ka wani ze zo, ko ka fito ka ɗauki mutum, akwai tsaro sosai dan tin daga bakin babban get din za ka fa ra cin karo da sojoji, motarsa ce ta danno kai tare da kutsawa, tin da suka hangi wannan motan ƙiran Rolls Royce baƙi, tin kafin ya iso bakin gurin suka buɗe mai get din ya shige da mugun gudu, sun san dai AA ne be da hankali sam koɗan yana ganin Mahaifinsa ya na da matsayi sosai a fanin siyasa, be bin doka ko kaɗan shi dai. cikin yanki ya nabda daɗi sosai dan be da yawan muta ne ga wadatan bishiyoyi, sannan ga ginin dukkan unguwa kala ɗaya ne sky blue da fari hatta napep din unguwan haka suke, Direct wani babban gida ya shiga bayan ya yi parking ya zuro ƙafafunsa waje sannan ya bayya, matashi ne dogo me kimanin 27yrs, ba fullatani me hasken fata ta manya idanu, gashi da gashi irin na fulanin usuli wanda yake kwance tsab, yana sanye ne da ƙananan kaya wanda su ka hau fatan na shi, a kallo ɗaya za ka sheda rashin natsuwa sa, rashin wadatanciyar ibadah, babban parlourn gidan ya shiga hannunsa ɗauke da wayansa, yana shiga ya tadda babu kowa a parlourn dan haka ya nufi part dinsa bayan ya koma ya ɗauko wani blanket a nannaɗe, yana shiga ɗakin nasa ya warware bargon a kan makeken bed din shi, take macce ta bayya kwance a sume, tsaki ya ja sannan ya dauko wani allura tare da yi mata a hannun, kallonta yake yi sosai duk da fuskanta duk ya sha bandage ta ko ina, infact yana tinanin harta brain dinta sai a hankali, ya ra sa meyasa yake jin haka daga gareta, ya na da ƴam mata da yawa amma be taɓa jin yanayin da yake ji akan wannan yarinyar ba wacce take a matsayin matar sa. **************** ************** Zuwa yanzu Shuraim da Kifayaty sun zama ɗaya domin kuwa har Allah yasa sun samu rabo, dan cikin har ya kai wata 3, ita Meerah kuwa na ta ya kai 5 mounth. Shuraim na ba ta matuƙar kulawa in dai yana gida dan yanzu weekends kawai ya ke yi a gida be da lokaci sosai, amma a haka suke ta gudanar da ƙauna abinsu. Sannan shuraim ya ne mi Auran ƙanwarsa ga abokinsa wato Kandy da Adam in da Pazar R yace " ai shi kan shi ya na da iko da ƙannan na sa." dan haka ya ba shi ita, kan cewa nanbda 5 mounth za'ayi bikin tare da Fancy wacce soyayya ta ƙullu tsakanin ta da M.D malamin makarantar su, Shuraim ya yi bincike ya ga ba shida damuwa sannan ya amince, sai su tweens wanda suma Allah ya ba su twees Yusuf da Yunus wato ya yayyanin Meerah wanda sun taɓa zuwa gidan anan ne suka haɗu, aikan suka ma Meerah magana ta ko shiga musu hanya har suka amin ce. END. ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿. [7/1, 17:27] sknt6428: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊 𝙍𝘼𝙎𝙃 Ɓ𝙊𝙔𝘼𝙔𝙔𝙀𝙉 𝙈𝘼𝙎𝙃𝙀Ƙ𝙄 Page 34. **************** ******************** "Salon RASH ya sauya sosai, ya de na kisa, sai dai datsan bankunan manyan muta ne a ƙasar nan, mun kasa ka ma shi sam, a yanzu zan cen da na ke muku tin watan nin baya da muka samu makama guda ɗaya amma kafin mu cin ma ƙudirin mu ya riga ya goge page din dan tashi za mu bi diddiginsa." Zaki ya kai ƙarshen maganan yana zama a meeting room din sai Ramlah ta miƙa, ta na sanye da hijab din ne har zuwa gwiwa, sannan ta fa ra da ce wa " Muna mai ba da haƙuri akan komai ace mutum ɗaya tak ya gagari rundunar mu, abin da mugun kunya, hatta jama'a zagin mu suke akan wannan case din, ina son na bada wani shawara akan wannan case." Gaba ɗaya muta nen suka ƙara ba ta natsuwar su. abubuwa ta furta wanda gaba ɗaya duk sun yadda sannan aka ta shi. Zaki ne ya fita zuwa haraban station din in da ƴan jaridu ke ta jiran futowansu, take suka kewaye shi kowa yana gefo mai tambaya, sai bayan da suka yi shuru sannan ya ce " A yau ne mu kai zama na ƙarshe akan RASH....." " Kun samu nasaran kama shine?." Wani ɗan jarida ya katse shi da sauri. "A'a mun dai yanke ce wa daga irin wannan rana mun aje case din RASH tin da babu wani ci gaba acikin aiki." " Aganinku wannan ba abin kunya ba ne ga dukka jami'ai na ƴan sanda?." Wani ma ya sa ke cillo tambaya, shi be san yawan magana, yana da damuwa a rashi sosai, kafin ya yi wata magana sai Meerah ta ce "Wannan ba jami'ai suka yanke hukunci ba saƙone da ga sama......" " Kun dai ga za?." " Eh, ko za ka da sa ne?." Ta ƙura ma wanda ya katse ta, daga haka suka bar gurin suna jiwo abubuwan da suke ta cewa a bakin motarsa suka tsaya tana mai ce wa " Please Zaki kadinga addu'a In sha Allah za ta bayyana." kai kawai ya ɗaga mata sannan ta huce zuwa motarta wanda ake ɗaukanta shiga ta yi suka bar wajen, shi kuwa ko da ya shiga nabsa motan zama ya yi ya kasa driving din tinanin in da Babynsa take ya ke, kuma wani hali take, wanda yanzu kusan 2 mounth ne da ɓa cewarta. tafiya tayi zuwa kano gurin dangin Maman Rabi to ta dai hau mota sun tafi amma can ba ta isa ba, hankalisu ya tashi sosai, da kowa ma an bincika amma ba'a ganta ba, a hankali ya ta da motar tare da nufan gida, yana shiga part dinsa ya fara zuwa ya yi wanka sannan ya koma parlour acan ya tadda kusan kowa na gidan sunata hira, zama ya yi a gefe guda yana duba wayansa da yaji shigowar saƙo tin ɗa zu, Sk shine sunan daya bayyana a saman saƙon sai ya buɗe lokaci guda "Hey Zaki, na sa mo wani makama akan RASH, zan so ko zuwa dare ko da safe na ganka." Be san dalili ba amma aduk lokacin da yake tare da Sk ya kan ji ya rage damuwa akan Ramlat, reply ya yi mata sai yaji muryan Fancy a kusa da shi ta na mai magana. "Uncle Umar ga abinci." kaman ya yi banza da ita sai kawai ya amsa ba ta re da ya ce komai ba, " Ya ka mata ka ci karya wu ce." " Ok." Ya furta ma Aunty wacce ke ta kallon sa, duk ya sauya acikin lokaci " Zaki, ban daɗe da gama kallon news ba, meyasa kuka bar wannan case din haka?." Cewa Pazar R, dan dukkan su suna daga gefe guda. " Saƙo ne daga manya akan mubar case din yanzu shi yasa, akwai wasu cases ɗin a gaban mu." " Amma haka za'a bar mugun iri a duniya." cewan Pazar M, sai shima Pazar Q ya ce " Hmmm Allah ya yi mana maganin sa." dukkansu suka amsa da Ameen. Sai da aka kira magrib ya fita. ******************* ******************* Sam ba ta yanani mai daɗi kwana biyun nan, ga ɓacewar ƙawarta, sannan mahaifiyar su Allah ya yi mata rasuwa, a lokacin har asibiti aka kaita dan ta shiga tashin hankali ma ra misaltawa, sannan tin daga wannan lokacin yanayinta ya sauya sannan ga tina wani abu shima daya addabe ta Tinani Zaune ta ke bayan sun dawo asibiti kan suman da ta dinga yi, sannan a nan ne aka ce tana ɗauke da juna biyu, shuru ne ya ratsa parlourn na su sannan Shuraim ya ce " Kifayaty na yadda da ke tin ba yau ba, nasan kina so kisan dalilin da yasa na ke nuna ni gurgune. Shin kin san dalili?." Tai saurin girgiza kanta dan tana son ta sa ni, kuma tana yawan tambaya shi amma be ce mata komai, sannan ya faɗa mata abu a kunne, wanda take bugun nunfashinta ya tsaya na wani lokaci, sannan take ɗan farin cikin na ta ya ƙare, take hawaye suka fara sintiri akan fuskanta sannan ta zabura ta miƙa tsaye tana girgiza mai kai, Rintse idanunta ta yi tare da toshe kunnuwanta, sannan ta durƙushe agurin tana mai kallon tsoro, amma me Hausa sun ce tsakanin mata da miji sai Allah, a take kuma a lokacin ya kuma faɗa mata dalilan sa da hujjojisa, anan ne ya samu ta natsu tare da ce wa " Yanzu kai ne RASH?, ina sonka amma gaskiya bazan....." da sauri ya haɗe bakinsu guri guda shima yana mai zubar da kwalla. " Ba zan iya rabuwa da ke ba har abada." " Kamin alƙawarin ka de na kashe rai." yaji maganar na ta a ba za ta, be da wani option sai ya amince, kuma be sa ke kashe rai ba dan hadisai ta jawo mai sannan ta yi mai wa'azi.. Cigaba Furzar da iskan bankinta ta yi sannan ta miƙe ta shiga kitchen dan yin giki saboda yau Shuraim ze dawo dan yau Saturday. Sai yamma ta kammala fried chicken rice da yam ball, tana gamawa ta shiga ɗakinta ta yi wanka da sallan magrib, tana zaune har aka kira isha'i sannan ta gabatar sannan ta koma gaban mirrow tana kallon yadda duk ta rame sannan ta ƙara haske, riga da wando na Pakistan ta sanya sannan ta koma parlour tana kallo a colours TV. END. [7/2, 06:19] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 35. **************** **************** Be so fita ba amma haka ya fice bayan ya hangi Fancy da wani mutum suna hira a akan wasu kuje wanda ake zama ashe iska, har ranshi yaji daɗi da ta fita a harkansa kuma ya na mata fatan alkairi. Be tsaya a ko ina ba sai wani ƙaramin gida a waje ya a jiye motan na sa sannan ya shiga gidan, madaidaicin ne wanda ya siya ma SK dan bincike, ɗaki biyu ne a gidan daga na me gadi da matarsa sai ɗayan wanda a can take, key yasa ya shiga parlourn wanda be da wani kaya da yawa, zama ya yi kan kujera yana kiran numbern ta, kafin ya kiran ya katse ta fito daga ɗaya da ga cikin ɗakunan biyun da yake gani, suna haɗa ido ta sakar mai murmushi shima ya maida mata yana ambaton Allah a ranshi, sanye take cikin riga da wando wanda kusan kayan ta sune duk ka, wando palazo ne baƙi sai white shirt mai gajeran hannu, sannan tayafa Black vail akai, bayanta ya bi suka shiga ciki tana gaida shi ya amsa, baban ɗaki ne mai ɗauke da kayan aiki su na'urori da abubuwa da yawa na aikin su. " Sir zauna ka gani." ba musu ya zauna sannan ta janyo wani system tana latsawa da sauri sauri " Da alama RASH ya mance ya bar mana babban alama, kaga ɗazu misalin 3pm wannan account din da aka kwashe kuɗin Abubakar Samir a TAJ bank wancan week din, kimanin miliyan 2, to shine ɗa zu ya tura ma wannan account din budu dari 8, wanda da na yi bincike na gane account na gidan marayu, sannan duk bayan wata ya kan tura musu kuɗi." Takai ƙarshen maganar na ta tana kallon Zaki da ya ke tinani akan maganar, sannan ta ci gaba da ce wa " Gobe sai kaje ka ƙaro binciken dan ina da tabbacin zamu sa mu wani alama, ba zan bar RASH ba, dole muka ma shi." " In sha Allah." Daga haka suka dan yi wani hira sannan ya huce zuwa gida. ****************** *************** Unguwan babu yalwan gidaje sosai, can na hangi wani baban gida wanda tin daga waje za ka san gidan ya kai ace mai gida, babban get ne kalan dari blue, haka launi gidan ma, compound din muta ne sun kai 15 wanda suke sanye da Uniform iri ɗaya kuma bana sojoji ba sannan bana polisawan ba, dari blue ne Uniform din sannan duk suna dauke da bindigu a hannun su manya manya, sannan har ta bayan gidan nan ma akwai wasu guards din, babba ne gidan sosai, can ƙafafuna suna kai cikin bababn parlourn din, wanda anan na ga Adam, Sunusi Skiddo, da spider, hira suke yi a tsakanin su suna cin gashashshen naman rago. " Nan da wata biyu komai ze ƙare zamu samu freedom, nima zuwa lokaci zan ne mi soyayyan yarin yar nan." faɗin Skiddo sai Adam ya yi murmushi dan ya tina wacce yarinya yake magana wato Beauty "Haka ne Allah ya nuna mana." " Ameen amma ni ma gaskiya zanso amin hanya a Familyn Boss, duk kunmin wayo fa." " Hahahaha to ko ni ba ta san ina sonta ba, gaskiya Adamsi ka mana hanya mana." " Karku damu, kai Spider sai dai mu ba ka beasty dan ita ce bata da tsayayye a cikin su 6 din, dan sauran ukun ba sukai aure ba." "Ai ni ko ma wacece in dai ƙanwar Boss ce, so nake na kwatanta halaccin daya min akan abubuwa da yawa." " Haka ne ai Allah ya saka ma Boss, mutun ne mai kyakkyawan zuciya ga tausayi....." "Masheƙin kuma ɓarawo." RASH ya furta yana gama sauka da ga 5 steps din da ke gurin na kwalliya, a tare suka miƙa dan ba susan ya fito ba, taku ya fara cikin natsuwa da kamala, yana sanye da gajeren wando ne sai ƙaramar riga, hannunsa dauke da mug na tea, zama ya yi sannan ya ce " Wato ku ƙannaina kuke so ku aura, hmmmm hakan ya yi kune amintattuna na san ku na yadda da tarbiyyan ku kuma kusa ranku a inuwa." take ya ciro wayansa tare da kiran wani number bugu biyu aka ɗauka a speaker ya sanya wayan sannan ya musu nuni da su zauna sannan suka zauna "Ina wuni Baban yaya." cikin ɗari ɗari ta furta sannan ya ce "Lafiya Hauwa'u, ina Hajara?." Beauty ta kalla Beasty tana mata alama da ta matso aikan ta matso tana ce wa " Baban yaya ga ta a gefe na." " Tom kuna jina." da sauri suka amsa da 'eh' dan suna tsoron kar ace wani abu suka yi " Acikin ku akwai wacce take da saurayi ne?." Tambaya ta yi masu wani banbara kwai haka ko da ma suna da ai cewa zasu babu aikan haka suka ce, sai dai ya yi murmushi dan yasan aikwai ɗin kawai kwarji yake musu, sannan ya ce "Na mu ku mazajen aure, sai dai ba yanzu za ku haɗu da su ba amma ku kula." daga haka ya katse kiran, ai kuwa su Adam murmushin su ne ya ƙara faɗaɗa sannan suka mai godiya, miƙewa ya yi ya ce "Ban san godiya kun san haka, Adam shirya mu wuce." ɗakinsa ya koma ya shirya sannan fito, tare da Adam suka fita sannan su Spider na take musu baya, ko da isan su haraban gidan gaba ɗaya mutanen gurin suka sara mai wasu na buɗe get, hannu kawai yake ɗaga musu har fuce a gidan. ******************* *************** " Yanzu wai Baban yaya shine yace mu ku ya tsaɓan muku mazajen aure?." " Hmmmm ke dai bari Kandy." " Ai ni na zaci wani abun na yi har na ce ni Hauwa'u yau zan sha bugu." dariya suka kwashe sai Karis ta ce " Kuce mu na da shagali a ce family of ƙanƙara za a aurar da classic babies har guda biyar, akwai abu fa." " Gaskiya kam akwai wasan Naira." " Baby wani Naira, sai dai dollars $." dariya suka kwace dan Butter yadda ta faɗa dollar din harda alama da hannu yasa suka yi dariya. END. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [7/2, 13:26] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 36. ****************** ************** Kamar kullum akan keken yake Adam na turashi har main parlourn, nan ya samu Hajiya da Mom, za ma ya yi suna dan hira shi kuma Adam ya fice, be wani jimaba ya shige part dinsa. Kallon take ta ji an shigo sannan ta san waye a hankali ta juwa manyan idanunta zuwa garesa, yana dai kan keken nan, yana mata murmushi, a ranta tana ai yana shi ko akan keken handsome ne, balle ma da taga ya miƙe ya sauke ƙafafunsa ya ta ko gabanta. "Sannu da zuwa." Abin da ta furta kenan tana kauda kanta daga kallonsa "Sam bakya kewar mijinki koh? Ace kwanana 5 bana nan amma banga kina zumuɗi gani na ba." " Hmmmmm kason ina yi kuma ina ƙaunarka amma komai dole na rage har nan da ɗan lokaci." " Shike nan amma ki rubuta ki aje wata rana za ki yi alfahari da wannan RASH ɗi....." " Shuraim ka ke ba RASH ba, wai ma mene ne meaning din RASH din nan?." Sai bayan daya zauna sannan ya ce "Da fari ban san sunana ya za ma sunan yana kama da Shuraim sai kawai a ciki na haɗa RASH, amma a yanzu zan iya ce wa R.A-RAMLAT, S.H-SHURAIM...." " Hmmmmm ba banza ba ka zama RASH, yanzu dai ka ajeshi a waje, shuraim kawai nake buƙata yanzu." " Tom an gama shine yanzu." ya fada yana riko hannuta. " Na san ka yi wanka kafin ka fito, muje ka ci abinci toh." " Toh Maman Baby, fatan yana lafiya?." " Uhmm lau yake abinsa." " Toh bara na kammala cin abin ci sai na duba lafiyan shi." abinci ta ajemai ya buɗe ya fara ci da Bismillah, sai bayan da ya gama saf, sannan ta ce " Fuskarta ta namin yawo a kwanya, tinaninta yana hanani sukuni, kewarta nake yi sosai." sai ga hawaye sun zubo mata hannunsa ya sa ya shere mata yasan dole ya da me ta saboda sun shaƙu sosai da Ramlat, gashi saura sati ɗaya bikinta sai ya ce " Kin san ba cikakken lafiya kike ba, bansan wannan hawaye kinji, Ni kaina na dage da bincike amma bansa sa'a." "Ni wallahi ko gawarta na kwammaci na gani na huta nasan ta koma ga Allah, amma yanzu ban san ko wani hali take ba halamaaa......." hannu yasa ya toshe mata baki sai ta yi shuru amma har lokacin hawaye na zuba daga idanunta. Hmmmmmm ba muyi komai ba fa dan yanzu labarin ze fara na da citta------------ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ******************** **************** " Kin san mu na da nisa bara na huce yanzu, jinai inason na zo na ganki ne, gobe ma still babu school sai Monday bazan iya hana zuciya abin muradin ta ba." Dariya Fancy ta yi tana miƙewa, har mota ta rakasa sannan suka yi sallama ya wuce. Direct sai Air Force Base ya nufa, security na du ba shi suka sara mai sannan ya shige, be tsaya a ko ina ba sai cikin gidan su, da sarsarfa ya shiga cikin parlourn, Dad da Maa ne zaune suna hira, sallama ya musu suka amsa fuskanshi ɗauke da yataccan murmushi, zama ya yi sai Maa ta ce "Daga gurin budurwa ka ke koh?." sai dai ya sosa kai sannan ya ɗaga ma ta kai "Kayi min maganan auren, kuma na yadda ina so kaban address din ta domin na yi bincike akan tarbiyyan yarinyar." faɗin Dad yana mai kallon Muhammad. "Ai Dad ƴarinyar ƴar mutum ki ce, kuma familynta sanannu ne, imfact kai kasan Mahaifin ta." " Uhm M.D go ahead." " Sunanta Fatima Abdulrasheed Ƙanƙara, wato ƴa ga abokan aikinka Pazar M da Pazar B, sannan ƙanwa ga gomman hajar nan Aliyu Haidar ƙan....." " WHAT ! mene? ƴan family of ƙanƙara ka ke magana kai kasan abin da ke tsakanin da ƴan gidan nan kuwa?." Dad ya fura a zafafe yana miƙewa tsaye, Maa har ta fara jin ƙanshin mulki na kusanto Babban yaron na ta amma mijinta ya kyawo wani zance na daban, ita gaskiya yarinyar ta yi mata, dan ta na son haɗa iri da masu hannu da shuni a ƙasar nan. " Alhaji a ganina bangai aibun haka ba, matsalan ku daban haka soyayyan su daban....." " Maa wallahi hatta iyayen yarinyar sun karɓe ni da ƙima, ko da na na ce musu ni ɗan Anas Chul ne sunji daɗi ba su nuna komai ba a fuskokin su." " Oho ni dai na faɗa ma ka, ka m canza shawara tin da wuri." Daga haka ya haye stairs sannan ya shiga room disa tare da kiran wani number budu biyu aka ɗauka. "Chul ya ka je gida" "Askira ba wanne yasa na kira ba, shin kasan wai M.D ƴar ƙanin Abdulmajeed yake so ya aura." na cikin wayan sai da ya yi gyaran murya sannan ya ce " Ƙanƙara family wai?." " Hmmm su fa." " Hahahahaha ka ce hanyan matsalanmu ta kawo." " Kamarya Askira?" Fuskan sa da matuƙar mamaki yake sauraran abokin na sa, sannan a dai dai lokaci ya gama zayyano mai abin da ya zo kansa, take na ga Child ya saki murmushi, sallama suka yi sannan ya koma Parlourn yana tafiya cikin sauri sauri sai ya ji Muhammad na ce wa. " Maa Please ki taya ni roƙansa wallahi na makance akan soyayata ita ma haka ......" " Na yadda." a tare M.D da Maa suka kalla Dad wanda ya zauna a in da ya tashi, sannan yaƙara tabbatar mai yana mai ɗaga kan sw alaman eh, Maa murmushi ta sa ki tana jin daɗi a ranta, har ta hango yadda zata sheda ma ƙawayenta. Sarai tasan Chul sannan ta san mugun halinsa, ta san tarko ze yi da yarinyar da aka kira da Fatima. " Meke faruwa ne?." suka jiyo tambayan daga sama, sun san wane ne Auta ne, dan haka dukkansu suka kalla saman suna mai sakar mai murmushi. tafiya ya so ma yi cikin wannan takun nasa mai ɗaukan hankali, har ya iso parlour din sannan ya zauna. " Auta ai ɗazu danaga motan ka na san ka dawo ban san na zo na ta kura maka shi yasa na barka dan kahuta." cewan Maa, sai Dad ya ce " Yaushe za ka tafi London din ne?." " Jibi zan wuce, kuma a ƙalla zankai wata 8 zuwa shekara ma " muryansa mai sanyi da ɗaɗi ya faɗa hakan yana kallon yayan shi. " 1year, no shi yasa tin ba yanzu ba na ke maka magana akan auren Salma yanzu kenan har sai ka dawo za ayi?." " Eh Maa." "Gaskiya ban so haka ba ya kake so na yi da Aminiya ta ?." " Is not my business." sun san halinsa sam be da mutumci wasu lokutan, miƙewa ya yi ya shiga kitchen jim ya fito ɗauke da Flacks na ruwan zafi ya koma ɗakin na sa. "Yaron nan sam be da hali, shi yasa nafi sonka M.D, be bin magana na hmmmmm." faɗin Maa tana miƙewa ta shige part dinta. Dad da MD ne suka hada ido sai Dad ya ce " Uwa da ɗanta baruwan mu da shiga tsaki." " Aukuwa Dad, na gode sosai da amincewar ka." Ɗaga kai Dad ya yi. Sannan kowa ya shiga saƙar zuci. Ya na shiga ya kulle ƙofan sannan ya shige bedroom can ya hangi bugun nunfashinsa, gadon ya hau yana ƙare mata kallo sai ya saki murmushi sannan ya kai bakinsa kunnanta ya furta wasu kalamai wanda tin da yake be taɓa furta ba kowa ba. " I love you Airah." sannan ya yi ma ta peck a kumatu, yana mata fatan samun lafiya cikin gaggawa.. END. [7/3, 12:05] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 37 *********************** ********************** Zaune suke a ɗakin mai girman gaske, su biyu ne kawai suna kallo juna tare da sakin ma juna murmushi. "Gobe zan sa a kashe sactaryn Aliyu dan haka ka shirya zuwa next week kaine za ka za ma sectary, daga nan sai mu fara tinanin yadda za mu kawar da shi." " Haka ne Chul amma zan so kafin nan mufara cusa ma sa baƙin ciki a ransa, ka ga munyi nasara sosai watanin baya, ya rushe makarantun mu, ya gini hosbital da makarantu sannan asibitin ka nan ma sai da yasa aka kulle....." " De na tunanin Askira, yanzu dai nan da wata 5 ne bikin daga nan sai mu cimma komai, na san yadda zanyi da ɗana kawai zansa Maa taje gurin boko ta sa a juye mai tinani." " Harna fara hango fuskokin Pazars, wai ina A.A ne?." " Gobe zebar ƙasar nan, kasan shi ai wai akwai wani abu da ya keso yaje ya yi ne, narasa yadda zanyi da shi, gaba ɗaya yadda kasan ba jinin Chul ba." "Sai haƙuri ai, Maman Salma ta faɗamin wai sai ya dawo za'a tsaida bikin na shi shi da Shaleleta (Salma)." "Eh Allah ya haɗa kan na su, kaga zuwa lokacin ai na san ta kammala karatun ko?." " Eh ta kusa saura kaɗan ai." Daga haka suka canza hirar tasu. ******************* ******************* Misalin 10:15am ya isa wani babban gidan marayu me suna TRUE CARING ORPHANAGE wanda yake cikin gari. Baban ogan gurin ya samu suka tattauna amma be samu yadda yake so ba, domin su dai tura musu kuɗi kawai ake yi ba tare da sunsan wane ne ba, harta yaran da suke rayuwa a gidan ya ɗan bincika ko zai samu wani yasan wani abu akan Rash amma ina haka ya gama ya fito yana ƙare ma marayun gurin kallo, mutane sosai ne a gurin, wasu na wasa wasu aiki wasu kuwa karatu, aciki sunada ɓangare mai yawa hatta ɓangare karatun akwai, na musulmai da arna, yana wuce wa, mutumin dake zaune da glass ya cire tare da ciro wayansa ta kira wani number, bugu biyu aka ɗauka sai ya ce. " Ina son ku haɗani da Shugaba." Daga cikin wayan aka ce. "Bara mu haɗa ku riƙe waya." shuru ya yi har aka kira number Rash, connecting aka yi sai mutum min ya ce " Shugaba barka da safiya, Baba sule ne shugaban gidan marayu, jami'ai ne suka zo tambaya akan ka yanzu, na nuna musu ban san komai akan ka ba shine jami'in ya wuce." " Toh, idan akwai abin da kuke buƙata kasanar ma Skiddo." Yana kaiwa nan ya kashe kiran na shi, sai Skiddo ya ce "Akwai abin da kuke buƙata ne?." "A'a komai akwai muna godiya." "Go de ma Allah." sannan ya katse kiran, shuru ya yi yana mai kallon yaran da ke wasa agurin, aran shi yana gode ma Allah daya turo musu Rash, dan tin da ya fara taimakon su rayuwan su ta faru, ya na yi masu komai, shi ya sake musu gini, ya yi makaranta a gyefan filin da ya siya a kusa da gurin, ya turo musu malamai, abubuwan daya yi musu ba su da adadi, amma har ran shi be son kallon da mutane suke mai na mugu dan Rash bawan kwarai ne, kuma ya na fatan yaɗuwa da shi. END. [7/3, 18:39] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 38. ******************* ********************* "Sk yanzu akwai wata makaman ta da ban ne.?" Sk da tinda ya shigo ya ce babu sa'a ta yi shuru tana mai tinani sai ta ce. " Gaskiya yanzu babu." " Amma kin san mene ne?." ta ɗago idanunta tana kallonsa ta ce " No sai ma faɗa." "Akwai abin da na ke so na gane akan Rash, bincike nake so kifaramin akan RASH din amma ba......" jin wayanshi ya fara ringing ya sa ya katse magana yana daukan number Meerah. " Aslm Meerah." sai ya yi shuru yana sauraren ta sannan ya ce "Ya Allah, wannan RASH din wannan bawan wai a ina yake ne?, Shike nan." Daga haka ya katse kiran yana da fe kansa. " Lafiya mene?." " RASH." " Me kuma ya yi?." Ta faɗa tana sauke nunfashi dan yanzu har jira ta ke ace ya yi ka za ba ta shakkan jin komai dan baƙaramin hatsabibi ba ne. " Kuɗi kimanin miliyan 15 ya kwashe a bank, ta ce yanzu za ta turo mana komai." " Ok." Daga haka ta miƙe ta shiga madaidaicin kitchen dinta wanda babu kaya da yawa aciki, futowa ta yi ɗauke da cup da plate ta ajiye a gaban shi. " Inaso na ga ka cinye komai anan, na ba ka 5mnt, kuma time din ya fara daga yanzu." kallonta ya yi sai ya ɗauka wayansa, take ta fizge sannan ta haɗe rai fiye da yadda fuskan na ta ya ke. " Sauran minti 4 da sec 45." jin haka yasa ya ɗauki cup din ya kai baki sannan yayfara cikin doya da kwai yana korawa da lemon tea, idonsa na kan agogo. " Done." ya furta yana kallonta, murmushi ta saki dan haka suke yi in dai ya zo ta ga alamun be ci abinci ba haka take mai kuma ya ke ci. " Duk ka rame, Ni kaina ina cikin damuwa da ɓatar ta, hatta wayanta da muka gano a ta dha yana wajena, da zaran na ƙalla sai naji kwalla a idanuna." Ts miƙa mai wayan na shi, maimakon ya amsa sai ya riƙe hannunta ya na ce wa " Na gode, ban san meyasa ba idan ina tare da kai komai na wa can za wa yake yi." " Nima haka ne kamin abubuwa da yawa a rayuwa ban san da me zan sa ka maka ba, na so na zama silan kama wannan dodon da ke addabar ƙasar nan, amma na kasa Zaki." " Ina ƙaunar ki Sk." tin ba yau ba ya kan ce mata yana ƙaunarta sai tayi mai murmushi hakan yau ma ta ka sance. "Na roƙe ki wata alfarma." ya samu leɓansa da furta haka badan ya san me kuma ze ce ba, da kai tayi mai alama, kuma ta natsu tana sauraran shi. " Kusan wata uku kenan, idan zuwa yanzu na yi wani auran nayi ma Ramlat adalci kuwa?." " Aganina ba ka yi ba gaskiya, dama dai ya kai wata 5 haka zuwa shekara shine kamata adalci." Ta furta kanta tsaye, sai yaji daɗin maganar na ta. " Toh idan har nan da zuwa wata biyar babta dawo ba za ki aure ni, ki maye gurbin ta a gareni.?" Tambayan ta doki cikin kwayanta sannan ta zauna gefan sa ta ce. " Da ba kai bane tsaf zan iya wanke mutum da mari, tsaf zan kalli cikin idon sa na ce sam wannan be da ce ba, amma kai ne, babban gatan ga ta na bazan ce a'a ba amma zanyi addu'an kafin lokacin ta bayyana." " Bakya sona ko?." " Hmmmmm Ƙaunarka kawai na ke." Daga haka ta shige bedroom ɗinta, lumshe idanu ya yi, yayi Istikara kan wannan lamarin amma Sk ita kaɗai yake gani shi yasa ya zaɓi faɗa ma ta ha ka. ************* ***************** Air Force Base Jigum jigum suka yi dukkansu su biyar ɗin suke zaune, Dad, Maa, M.d, sai mata 2 wa'inda a kallo ɗaya za ka ga tsananin kama su da Maa, dan ƙannanta ne, ita ce babba sai Hafsa da Halima, amma ta girme su sosai, tsakanin su shekara biyu ne, Hafsat 26 sa'ar A.A sai Halima 24. Tin suna yara suka dawo gurin Maa da za ma dan iyayen su sun rasu, ta riƙe su tsakani da Allah dan ita kaɗai mahaifarta ta haifa sai ta mutu, gurin Hajiya Baraka ta taso cikin kulawa a lokacin Baraka na da shekara 18 amma ta koma ma Maa mahaifiya, da yake yarinyar ƙanwar Mahaifarta ce, bayan wani lokaci sai kawai ta auri mahaifinta ko a lokacin Maa na da shekara 8, sannan ba ta haihuwa har Maa ta yi aure dan sun fidda tsammanin za ta haihu. " Yaron nan wai me ke damunsa ne? Tin jiya ya bar giɗan nan kenan, na ra sa ya zanyi da Auta wallahi, yanzu ya wuce London din kenan babu sallama?." Maa kaɗai ke ta zazzaga masifarta ita kaɗai babu wanda ya ce ƙa la, dan duk yadda A.A ya za ma ta na da sa hannu dan ita ba ta kwaɓa ma yaro balle shi. " To ya za muyi sai addu'a kawai amma be kyauta ba gaskiya." faɗin M.d sai Hafsat ta ce " Allah ya tsare mana shi." dyaga haka ta gyara veil ɗinta wanda da shi ta shigo gidan sannan ta nufi part din su ita da Halima. " M.d je ka kwanta dare ya yi." a tare shi da Halima suka miƙe tare da barin gurin. Sannan Dad ya ci ga ba da ce wa. " Tinda ya ce mana ze tafi ai yayi ƙoƙarin ma, hala yanada babban aiki a can din ne." "Hmmm Alhaji yaron nan maganin shi zanyi da wuri, kafin ya dawo zan sa ka daura mai aure da Salma, sai na ga ta tsiya." " Maa duk yadda ki ka ce ai." END 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [7/3, 19:27] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 39. **************** ************** ROYAL HOSPITAL WHITECHAPEL RD, LONDON E1, 1FR, UK Sanye yake cikin kayan likitoci, shi da wani doctor ne suke magana cikin yaren turanci. *"Mr. Alexander, you know I didn’t specialize in matters of the brain, that’s why I brought her to you, because I trust your professional experience." " Mr. AA don't worry." Daga haka ya mai da fuskan sa kan Airah wacce ke kwance, nunfashi kawai take saki a hankali. Fucewa ya yi ya koma masaukinsa wani hotel da ke opposite da asibitin. ******************************* BAYAN WATA BIYAR A yau ne aka ɗaura auren ƴammata shida daga Familyn ƙanƙara, Hassan, Husaini, Fatima, Khadijah, Hauwa'u da Hajara. Har dar da Zaki shi ya aure Sk bi sa tsayawan Pazars da Aunty, An sha shagali na kwana bakwai, sai dai akwai abubuwa da ke kewa da wasu acikin ƴam matan wanda ba su sa ni ba. Zuwa yanzu Ramlat da Merah sunyi nauyi sosai. Taro ya tashi lafiya sai dinner daza'a gabatar kafin ko wacce a kaita gidan auren ta. ************* *************** Tsaya wa baku labarin gurin taron ɓata lokaci ne, amare na gyefe guda haka angwaye ma. hatta Babban yaya yana zaune daga gefe guda, shagali ya kai shagali, amare sun so su sha rawa amma babu dama Babban yaya ya hansu sa kewa. Hatta Gomna guda da wasu manya manya mutane sun halacci wannan taron. " A ganina ba sai ka hukunta su ba ka barsu da halinsu dan Allah Baby." Ramlat ta faɗa da sigar roƙo, Shuraim da ke kallon ta ya ce. " Karki damu Khadijah, Hauwa'u da Hajara kawai ne, banda Fancy a cikin su dama banda twins." " Please." " Hmmmmm na ɗan watan ni ne kawai." Daga haka ta bar magana. Misalin 10pm aka tashi sannan motoci suka ɗauki amare. Kandy a iya saninta ta san iyayen Adam sun rasu dan Babban yaya shine ya tsaya mai akan komai. Ita aka fara kai wa wani ƙaramin gida mara fasali, gidan zaman mutum ɗaya ne, Babban yaya shi ya musu kayan ɗaki, dan haka ba suje ganin gida ba sam. Ƙawaye sai ƙananun magana su ke, dan ace wan Kandy babu country da be je ba sai gashi an kawo ta gida wanda babu nepa aciki. Layi ɗaya ne tsarkin su da Hauwa'u zan iya cewa kwanda gidan Kandy ma dan ita Hauwa'u gidan ba ruwa sai well sannan ba nepa, ƙananun ɗaki biyu, kitchen da ba yi duk suna waje. a layi ɗaya suke da Hajara, dama dama na ta dan ita get ne a gidan amma ciki kuwa sai a hankali, amma bayinta na ciki sai dai ita ma babu nepa babu ruwa har rijiya babu. Kowa abun ya ɗaure mai kai ganin yaƴan manya amma sun ƙare gidaje marasa fasali Alhamdulillah Fancy cikin gidan su Chul aka ajeta, gida mai rai da lafiya, sai dai uwa uba shine in da aka kai Twins wato gidan su Meerah KK GRA.. Tin a mota Meerah da Ramlat ke ta dariya ƙasa ƙasa har aka mai dasu gida, part din Ramlat meerah ta zauna suna yin dariya san ransu, sun san ba komai yaja musu haka ba sai tsabar raina Ramlat da su ka yi suna ce mata ƴar talakawa, harta a gaban friends dinsu suna wulaƙanta, shi kuma Babban yaya ya na son ya koya musu darasi me kyau. Yaso harda Fancy amma ita ya barta, abin da be sani ba shine ita Fatima Allah ne da kansa zai nuna ma ta ishara. Aunty da wasu ne suka kai Sk sabon gidan da Zaki ya siya a gefan na Familyn ƙanƙara, cikin aminci suka barta sannan su Aliyu aka raka ango gurin amarya. ************* ************** Unguwar mai dabino Gidan Kandy, kuka take yi kaman ta yi hauka, yanzu wai a wannan gidan za ta rayu, tina abin da Babban yaya ya ce musu ɗa zu da rana tayi "Ni Shuraim a yau mun aurar da ku kuma ina mai janyo hankalin akan aure dan kunsa shi aure bautan Ubangiji ne, ko da wasa kar naji complain akan ku, duk in da Allah ya kai mutum ya yi hakuri dan yafi wasu, ba zan ɗauki yaji da mata ke yi ba haka saki duk wanda ta sa aka saketa to ta ne mi wani gidan, sai dai in da babban dalili ne." Sa ke rushewa ta yi da kuka, tana mai jiran Adam, aikuwa can sai gashi cikin manyan ka ya, abokansa na wucewa ta cire mayafin na ta sannan ta ce " Ya Adam bangane ba, me na ke gani? Ina ne nan?." Har ranshi wannan hukunci Babban yaya ya yi mai tsauri, duk da darasin rayuwa yake son ya musu amma be so ta haka ba. " My sweet Kandy, wannan shine gidan da na mallaka, na so na ne mi haya amma banda kuɗi duk a lefe suka ƙare." "So kake ka ce anan zanyi rayuwa, babu fanka babu AC. How?." "Kandy sa ta kikeso na yi ne ko mene?....." " Ina kuɗinka? Duk aikin da kake da Babban yaya ba'a biyan kane?." Dariya yake son yi amma ya haɗe rai ya ce " Ni ɗan rakiya ne, kuma nasiya fili ai karki damu zanyi gini soon." Kuka ta ci gaba da yi mai sauti, sai ya ajiye ledan ɗaya sannan ya buɗe ɗayan dan guda biyu ya shigo da shi, " Kinga shi yasa na siyo mana fitila me chargi, a cike yake ma." ya faɗa yana kunnawa take hasken sa ya bayyana dan dama wayarta ta kunna flashlight. " Ya zanyi na shiga uku na, Ya Adam meyasa ba ma faɗamin ba ko Pazars na tambaya su baka wani gida amma nan sam be yi ba." " Khadijah ke ba yarinya ba ce, idan kina so na to idan kuma ba kyau sona, auran ai ba dole bane kuma......" da sauri ta toshe mai baki da hannunta wanda ya ƙawatu da zanen lalle mai shegen kyau sannan ta ce. " Shike nan naji kasan ina sonka dai." Ya daga kansa, Rungume ta ya yi yana ƙara ƙaunata, har shi ze so ta sauka akan ƙyaman talakawa, ze so ta dawo yadda ya ke fata da Babban yaya. **************** ******************** Abin da ya faru a gidan Kandy shi ne ya faru a gidan Hajara da Hauwa'u, gashi sun kamu da soyayyan Skiddo da Spider, haka suka kwana suna kuka, tare da jin babu daɗi akan ƙaddaran da ya faɗa musu. END. [7/4, 17:53] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 40. ******************* ***************** Air Force Base Zaune take cikin babban mayafi, tana tsugunne ne a gaban wacce ke amsa sunan Uwar mijinta da ƙannanta biyu, sai mijinta a gefe, tamkar ba ita ce wacce suka taɓa zuwa dan gaishe ta ba, ta dinga rawar ƙafa akansu ita da Fancy da Beauty ne suka zo a lokacin. Tin da M.d ya kirata tun daga murya sa taji ya sauya mata dan cikin taushi yake mata magana amma ɗa zu kamar ba shi ba. sannan tin data fito zuciyarta ke ci gaba da bugawa sannan balle da Maa ta fara furta. " To a wannan gidan dai dokana ne ke aiki sai na Auta wato ƙanin mijinki, idan na ce abu to ba'a mu sa wa, kije ki kwanta yanzu gobe misalin ƙarfe 7am ki fito kisame ni dan jin dokokin na wa da fara aiki da su." " In sha Allah Hajiya Maa." Daga haka M.d ya ɗa gota suka nufi part din su, suna shiga ya ce. "Please Fancy love, ki bi uwata sau da ƙafa kinji." baƙara min haushi ya ba ta ba dan haka ɗaga kai kawai tayi, shi kan sa be san meke damun sa ba, za ma ya yi yana da fe kansa, sai ta ce. " Ba ka da lafiya ne?." " A'a lafiya na ke kawai naji kaina na ɗan min ciwo ne." ya faɗa yana riƙo hannunta, ido cikin ido suke kallon juna, irin kallon soyayya nan kallon ƙauna, kallon me isar da zazzafan saƙo. *************** ****************** Sallah suka idar sannan ya kama kanta ya yi mata addu'a wanda ya zama sunnah ga ko wani ango, abubuwa akan addini ya tambaye ta kuma cikin natsuwa ta ba shi amsa, har rashi yana mai farin cikin samun ta a matsayin mata, ya na da kyakkyawan yaƙini akan ta domin kuwa ya na so ya haskaka rayuwar ta da haske me yawa, ya wanke wannan duhun da ya ke cikin rayuwarta. Bayan sun ci abinci sai ta kalle sa ta ce. " Na tina Ramlat baiwar Allah, haɗuwan mu uku kawai amma sai nake ji kaman jini na ce ita, komai na mu ɗaya, murya, jiki, tsayi abu biyu kawai na iya fahimtar banbancin mu shine na fita zafi dan ta fini tsoro, sai yawan sakin fuska dan ko da yaushe murmushi za ka ta nayi." " Haka ne, na so da muka koma gurin Babanta ya ce kema ƴar sa ce sai dai ya ce shi Matarsa mace ɗaya kawai ta haifa, baiwar Allah ba ta ƙarewa." " Ina mata addu'an idan tana raye Allah ya bayyana mana ita, idan kuma ta rasu Allah ya haskaka makwancinta da Rahman Allah." Sai suka haɗa baki suka ce 'ameen'. Sannan suka shiga faranta wa juna har Allah ya basu ikon mallakan juna, jini ya gauraya, sunnah ta afku cikin tsarin shari'an addini. (Daga pretty SK 😍 Amare fatan Alheri, sai na zo cin chinchin da dubulam 😋) ******************* ******************* " Allah sarki Abbuu, Allah ya sanya alkairi." shuru ta yi tana sauraran na cikin wayan sannan ta kuma ce wa "Shike nan tin da ka sanar musu, yauwa a huta lafiya Abbuu." Daga haka ta katse wayan tana jin farin ciki a ranta, Abbu ya aura wata baiwar Allah a saudiyya dan watansa 4 da koma wa can dan ƙaro ilimin addini kuma yana koyar da ƴan sanawiyyah (ss Islamic level). **************** *************** Unguwan me dabino Tsaye take jikin window tana hange matan da suka yi layi a bakin rijiyan gidan suna ɗiban ruwa, mamaki take yi yadda ta ga mata duk cikin yanayin ƙazanta, ga kwata daga gefan rijiyan, tana so ta fita dan shiga kitchen ko tea ta haɗa, amma ta kasa fita koma wa bedroom ta yi tana mai jin kaman ta koma gidan su, kwance yake yana barci hankalinsa kwance, tsaki taja a fili tana kallon Sunusi mijinta, tana son sa tana ƙaunarsa amma sam ba ta san talaka ba ne sai jiya da aka kawota ace kamar ita Beauty amma ya za tayi haka Babban yaya ya so ai, zama ta yi gefansa ta ɗauki wayanta, take ta shiga contact ta kira Beasty. Bugu biyu ta ɗauka, gaisawa suka yi sannan suka hau wa juna jaje gashi Babban yaya ya umarci ko meke faruwa kar su kira kowa a gida. Beasty wacce ita yanzu Mubarak Skiddo ya ga ma ɗibo mata ruwa a ɗan wani fanfon maƙotan su. "Ni beauty babban matsalan shine girki wallahi ban iya ba, ya zan yi?." "Beasty kenan ai sam mun cu ci kanmu, muna kallo Twins suka dage da koyan girki, mu dai sai ce wa ai gidan Naira zamu gamu ai." taji hawaye ya gangara mata, " Hakan nan za mu daure ko ya ya ne mu girki, na kira Kandy ita ma abun babu da ma." Daga haka suka katse kiran na su. END. [7/5, 14:27] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 41. ******************* ******************** Air Force Base Sai 7:30am ta samu barchin ya bar idanunta, miƙewa ta yi dan ita abin da Hajiya Maa ta ce ma ta, da sauri ta zura hijab dinta ta nufi stairs, a Parlourn ta hangi Maa da Halima, gaishesu ta yi amma basu amsa ba, cikin kakkausar murya Maa ta ce " Wato ke ƴar iska in ce 7am kifi to sai 7:30am, kika shanyani kamar wat ta dabba." "Hajiya Maa Please ki ya ƙuri, makara na yi." Ta furta dan a samu lafiya kuma ɗan jiya ta shigo gidan. " Ki ɗaga mata ƙa fa yau dan Allah amarya ce da." ce wa M.D yana sauko wa daga stairs, ta ra sa gane me ke faruwa a gidan wai meyasa haka ne, jiya ta zo gidan amma ba ta shiga a sa'a ba sam. Hawaye ne ma su zafi suka gangaro mata ta share tanajin dokokin Maa gareta. " Girki safe, rana da dare ke ce, mu ɗauke miki shara amma wanke-wanke ke ce, kowa da abin da yake son ci dan haka list ne abinci kowa ya kan ja mark ne da daddare akan abin da yake son ci da safe, a ƙalla 8am agama breakfast, 1pm na rana, sai 6:30pm na dare." Jita yi zuciyarta har ta tsinke akan wannan dokan, shikam M.d yana ji a ranshi babu daɗi amma sam babu daman ya ce ƙa la. " Yarinya ta kin ta shi lafiya?." Da sauri ta ƙalla Dad wanda tin ba yau ba, ta san shi, a da can har gidan su yana zuwa, murmushin da ya yi mata ne ya sa ta ɗanji release. Zama ya yi yana kallon Maa ya haɗe rai. "Amarya ce fa ya ka mata kibarta ta huta na wasu lokacin ko ba haka ba." "To in ta huta na yau wa zak girka mana abinci dan tin jiya na sallami larai mai mana girki." ƙarara yya fahimci Maa ba ta ma ra ba da ita, shi kuwa M.d yana daga gefe kaman saƙaƙo ko tari baya yi. " Shike nan zan shiga amma zan so na masu me ta ya ni dan ban iya girki ba, ba na yi a gida, karatu shine......." "Ashe da aiki, ba ki iya girki ba?, Maa karna makara na wuce." Halima ta miƙe ta fice. " Lallai ma, shiga kitchen din ganinan zuwa." Daga ta miƙe ta nufi in da take sa ran nan ne kitchen ta shiga, ita za ta iya rantsewa ko ɗauka abu ba ta yi a kitchen sai dai ta aika su Baby, ta so ace ta daure ta koya girki dan wata uku me koya musu girki ta zo ta yi, amma ba ta ta ɓa zuwa ba. A parlour kuwa Dad ne ya kalli Maa ya ce " Ya yi wuri Maa ina laifin kibari ta yi 1 week, dan Allah kibari ta shaƙu damu na wani lokaci dan komai ya tafi yadda ya da ce." " Shike nan kai M.d ja ta ku nufi part din ku, amma 1 week kawai na ba ta." har ranshi yaji daɗi dan haka ta sauri ya shiga kitchen, ganinta a tsaye tana zubar da kwalla yasa ya rungumota ta ba ya ya na ce wa. " Muje ɗaki." hannunta ya ja har suka ratsa Maa da Dad suka shiga part dinsu. " Me ke faruwa da ni ne?, Shin dama Maa ba ta sona ka aure ni? Meyasa na ke ganin tsana ƙarara acikin kwayan idanunta?." Ta jero mai tambayoyin ta na fizge hannunta, shi kanshi be san mai ze ce ba sai kawai ya zauna kan sopa ya kulle idanunsa. ******************** ********************** RHYENO ESTATE MILLINIUM CITY Gida har yanzu a cike yake dan yau wasu duk za su wuce, Aliyu da Meerah ne na hango a gefan Main parlour suna magana ƙasa ƙasa, saboda kar su da me mutanan da ke kai da kawo. " Please da naje zan ɗauko na dawo." " A'a ki dai aika driver kawai, kin san kin shiga watan haihuwa, so kike ki haifamin Baby a mota, shekaran jiya kin fita haka jiya sannan yau ma, ni dai a'a gaskiya." Haɗe giranta ta yi tana gyara gyalen doguwar abayanta tana ce wa. " Na bar magana ma, shike nan ka yi tafiyar ka kawai, ina wani ni sa nan da K.K Hajiyar mu ce ta ƙirani ɗazu , kuma zan sa matar Babban yaya ta rakani." Ganin ta dage kuma koya hanata sai ta je dan ta yi niyya, amincewa ya yi tare da fice wa da ga gidan. Ta san Babban yaya ba ya nan dan haka ta nufi part din Ramlat, a parlour ta same ta tana cin Indomie, gaisawa suka yi dan yanzu da ba ta zuwa ko aiki kusan anan take wuni su sha hira. " Da gyar ya barni, zuwa Azahar sai muje." " To shike nan ni dama na faɗa mai." Hira suka shigayi suna yi suna dariya, sai ga Hajiya ta shigo, gaisheta suka yi ta amsa sannan ta ce. " Meerah in babu damuwa za ku iya biya wa gidan Fatima dan kai mata saƙo tin da han ya ce in ya so su sauran tin da nasu gidajen da nisa sai na aika mu su na su." " Karki damu Hajiya zamu kai dukka, kaman na ji Aunty Hajjo za ta ganin ɗaki koh?." " Eh su uku suke so suje dan ba su je ba jiya gashi gobe za su koma ƙanƙara." " Su shirya kawai muje dukka tare." cewan Ramlat, cikin ɗan nishaɗi Hajiya ta fice dan sanar ma sauran. END. [7/5, 14:18] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 42. *** *** *** *** Sai da suka yi Sallan Azahar su ka ɗau hanyan K.K, da ya ke mota biyu suka yi harsu Baby sun haɗu dan su ma jiy ba su je ba. Suna isa me gaɗi ya buɗe musu ƙofa suka shiga dan a waje suka bar motocin, gidan an ƙara gyara shi saboda auran Twins ɗin, akwai ƴan mutane nan ma sosai, gaishe da kowa suka yi aka zauna aka gaisa, sannan amare Hasty da Husty suka fito cikin shiga iri ɗaya dan akwai walima ƙarfe 4 a gidan. Masha Allah ɗakin su sunyi kyau komai na su iri ɗaya sai da colours akan sauya wani, manyan parlourn me ɗauke da two two bedrooms, hatta Yusuf da Yunus sun zo an gaisa. Sannan Baby ta ba su saƙon Hajiya da Momcy sannan suka ɗauki hanyan gidan Fancy, ko da suka isa babban Get din Unguwan sai da aka kira gidan su Askira din sannan aka bari suka shiga. Suna isa suka fiffito suka shiga babban gidan. Tin a compound din za ka san giɗan ya ci ace gida, duk da be kai kyau ɗin na su Meerah ba amma yafi na su girma. a parlourn suka sauka in da Maa ta dinga rawar kai da su kaman ba ita ba, hatta Amarya Fatima abin ya ba ta mamaki yadda ta ga Maa na yi mata cikin mutane. Kowa sai jin daɗi ya ke ganin Fancy ta yi sa'ar Uwar miji mai sonta kaman su Twins ɗan Hajiya na ƙaunarsu. Ko ina sun ka shiga kuma ma sha Allah sannan suka ba ta na ta saƙon suka fice. Fancy dai ta na kallonsu ta balcony har suka wuce. Jita yi Maa na kwaɗa mata kira, da sauri ta koma parlourn. " Maa ga ni." ta faɗa da ɗarɗar dan har yanzu ba ta ga ma fahimtar in da Maa ta ke ba. " Uban wa zai tattare parlourn, kin san mai aiki ta wuce, in za ki daure ki daure ki koya aiki cikin ɗan lokaci, dan nan da 1 week za ki amsa girkin gidan nan, kwanda ki koya dan ba za mu ci mara daɗi ba." Ranta a ɓa ce ta tattara komai tana aiyana yadda za'ayi nan da 1 week ta iya girki. ayyana yadda za su kwasha ƴan kallo ta ke a gidan nan, dan in dai rashin mutumci ne an ba ta a ward dan hatta Kandy ma ta sa ra mata. ******************* ***************** Unguwar mai dabino Tinda motarsu ta shiga unguwan, su Karis ke ne man ba'asin in da za su, a wani gefan ƙaramin gida suka yi parking in da har yaran unguwa sun za ga ye motoci biyun suna kallo, da yake ta kan layin su Hauwa'u suka fara shiga, duk da taimakon driver da ya kai dan da shi a masu kai amare jiya. Gidan Hauwa'u suka fa ra shiga in da tsakar gida ma su ɗiban ruwa a rijiya sun gama hargitsa ma ta, kuma Mubarak ya ce baya son ƙazanta dan haka ji take kaman ta yi ihu ha ka dai ta ɗauki tsintsiya ta hau shara wanda rabon da tayi har ta mance, jin sallaman ƴan gidan su hakan ya sa ta sa ki broom din ta nufa ƙannanta da ƴan uwan su. da ƙyar parlourn ya ishe su, dan ƙarami ne kujera biyu ne kawai ya ɗauka. Mubarak ya fita tin safe sai ƴan uwan wa in da suke ɗan leƙowa a na ta mata san barka duk da ma wasu gulma, Haushi da ta kaici duk ya kaita ƙarshe, Karis ce ita ma da abun ya kaita ƙarshe ta ce. "Beauty wai anan za ki rayu? Impossible sai ka ce ke ji." " A gaisheki, no light, no water, and see the place ko masu aikin mu gidajen su is better than this house." Butter ta kai aya tana gyara zamanta akan gadonta dan su hudu suka shiga ciki. "To menene a ciki, ai shi aure bautan Allah, wata rana sai labari." " Baby ban san me yasa kanki kullum a doɗe ya ke ba, Babban yaya kaɗai na ke tsoro da wallahi yau zan ko ma gidanmu, ku kalli wannan tsinannen gidan, bazan iya rayuwa a ciki ba." Daga haka suka dinga jajanta ma ta tare da zayyana mata yadda gidan su Twins da Fancy ya ke. Basu jima ba suka gangara motansu zuwa gidan Beasty, nan ma sauka suka yi, Baby ta yi Knocking sai Beasty ta zo ta buɗe tana fatan ba ƴan school dinsu ba ne dan ɗa zu wasu suka zo harda yin video abin ya ɓa ta mata rai sosai. " Sannun ku da zuwa." ta furta tana rufe gidan, su Hajiya Hajjo, Aunty Yalwa da Baabaa Harira suka amsa cikin sakin fuska sannan suka shiga cikin ɗakin na ta, yana da girma na ta dan ya ɗauke dukka kujerun ga bayinta a ciki ha ka kitchen ma, sai dai gidan ginin ƙasa ne irin na da, sannan da a basto aka yi rufin gidan. Nan ma ba su juma ba suka bar gidan bayan ta gama shan kuka a gaban su Karima wai ashe Sunusi cutar ta ya yi gashi Babban yaya ya ce babu sa ki babu ya ji. Su dai su Ramlat da Meerah sai kallon da murmushi suke yi. Kandy nan ne gidan ƙarshe da suka yi niyyan zuwa, shiga suka yi, ya-salam abin ka da uwar ganda gidan nan yadda ma su ɗiban ruwa suka lalata haka ta barshi, ciki su ka shiga suka zauna da ya ke Kandy akwai faɗin rai da zurfin ciki, sam ba ta nuna wa su Butter damuwanta ba duk da sun ga haka daga ƙwayen idon ta dan sunyi ja sosai... Har sun ɗau hanya dan sun fito kan baban titi, sai Ramlat ta ne mi su ɗan sauke ta ta gai da Maman Rabi duk da sai an shiga layi na biyu, babu musu suka je tare da Meerah suka shiga, Maman Rabi da ke jajjage a turmi, ta shin fiɗa mu su ta barma suka zauna, gaisheta suka yi ta amsa sannan suka kuma ma juna jajen ƙawarta wacce a yanzu ta kai wata 8 da ɓa cewa. sallama suka yi mata suka fita, jikinsu ya yi sanyi sosai dan da ta na nan da harda gidanta za su je. Ana kiran magrib suka isa gidan na su amma sai suka leƙa gidan Zaki dan ba lalle su kuma fitowa ba, cikin fara'a Sakeenat ta tarbesu dan tin safe Baby ce kawai ta shigo mata, daga ita sai Zakin ta. Ba su jima ba suka fito suka shiga na su gidan kowa ya yi part din shi dan hutawa. END. [7/5, 14:18] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 43. ************* ***************** a ckin watannin baya abubuwa duk sun faru a ɓangaren RASH kuwa, har sau biyu aka kusa kamashi amma ya zulle, hatta da tsan bankunan yarage yi yanzu, sai dai ko ya yi a ɓoye ya ke yi baya bayyanawa a duniya, duk da in dan a ɗauki gawan ana gane kisan RASH domin duk kisan da ze yi yakan manna stam na wani star mai ɗauke da kalmomi 4 (Rash). Harkokin sun bun ƙasa a yanzu ya haɗa kai ne da wata ƙungiya na safaran miyagun kayan ma ye da sai da matan Nigeria zuwa wa su ƙasashen, kimanin wata 2 da shigarsa daban ke nan wanda ya haɗa da wasu manya mutane a ƙasar Nigeria sannan da wasu ƙasashen, amma ba su ta ɓa ganin fuskar shi ba imfact Skiddo shike halarta duk wani meeting shi kam yana daga gida ya ke kallon komai ta cikin ƙaramin na'urar da ke glass din Sunusi Skiddo. A yau ma wani meeting din yaje wanda a garin Legos aka yi kusa da border, get aka buɗe mai, bayan sunyi parking suka fito, Skiddo wanda ya sha baƙaƙen kaya hatta fuska shi a rufe yake, ta ku yake cikin natsuwa shida jagororinsa a ƙalla sun kai mutane 30 dakkansu ɗauke da bindigu, kuma sunyi wani style gurin tafiyan har sai da Skiddo ya shiga babban fadar Rash din sai suka juya zuwa in da suke zama. Da Sallama ya shiga Adam da ke kallon haraban gidan ta cikin cc tv camera,, ya amsa sallaman sannan sai Adam ya ce. " Wannan takun fa mutumina?" Dariya ya yi ma ra sauti ya na ce wa. "Takun Uban da ba kenan Damusa (Adam)." Dan haka suke ce mai wani lokacin. " Gaskiya zaman na ku ya bada citta, kai da RASH ya ce kar kaci komai a can shi ne har da shan drink sannan ka ci kaza." Faɗin Spider ya na za ma gefan Adamsi. shuru Skiddo ya yi dan ya tina an ce kar ya ci komai dan mutanen gurin ba abin yadda ba ne, shikam Adam tina yadda suke kallon Video din ya yi, dan janye ƙyallen bakinsa ya yi ya ci kaza har da bar baɗa yaji sannan ya kora da Laziza drink. " Boss ya ga video ɗin?." Yya tambaya jikin shi ya yi sanyi, sai Spider da Adam suka kwashe da dariya sosai dan yadda Skiddo ya koma kaman abun tausayi. " Dariyan me kuke yi?." Sukaji muryan Rash daga ƙofan ɗakinsa sai suka sassauta muryan na su, sannan Skiddo da yake a tin zire ya ce. " Boss wai dan na ci Kaza da lemu shi ne suke min dariya wai za mu haɗu da kai." Sai da ya zauna a su kuma suka miƙe amma yana musu wani kallo duk suka zauna. Hannu ya miƙa ma Skiddo alaman clap da sauri ya miƙa saka yi clap tare da murmushi sannan ya ce. " Ai da be ci ba za su zarge shi, shi yasa na ɗaura Skiddo a cikin ku saboda shi wani lokacin be jiran umarni na, da Spider ne sai ya kira ya ne mi permission, kai kam Adam cin ne ma ba za ka yi ba kwata kwata." sai suka kalli juna suna kallon Skiddo da yake ta wani shash shan ƙamshi. " A din ga kula da ni, dan ni na musamman ne." Skiddo ya faɗa ya na miƙewa sannan ya kuma ce wa. "Naman ya yi daɗi fa na so na tambaya a wani restaurant aka yi sai na share kawai." " Me ya hana ka tawo da shi ragowan na ka tin da na ga ba ka tauna ƙasusuwa ba." cewan Spider da sigan tsokana sai Adam ya ka ma da ce wa. " Uhmmmmm yaro kenan, wani abun sai yara ko Sunusi?.." " Haka ne Damusa." da yake duk sun girme Skiddo din sai ya haɗe rai dan shi akwai san girma kaman gya re. "Mutumi na zo kusa da ni gyalesu." muryansa mai daɗi ya furta cikin sanyi sanyi, kusa da RASH ya zauna dan shi kaɗai ke haɗa kafaɗa da shi banda su Adamsi dan su ko yace su zauna ba sa iya haɗa kafaɗa da shi. " Yaya Rash next week za mu haɗu a ƙasar Chadi yanki zufl cikin hotel din Dream Hotel, room number F27." murmushi duk kansu su ka sa ki dan jin abin da Skiddo ya ce dan da ma wannan rana suke jira. " Shike man ku zama ready kawai, ku tafi gidajen ku, dare na yi kuma kun barsu ba security, zuwa gobe ina son ko wacce a samu a maƙala mata securitya ɓoye." " In sha Allah, amma ina son na ce wani abu." Rash ya yi ma Adam alaman yana jinsa sai ya ci ga ba da ce wa "Baban yaya, Kandy da gyar ta iya barci a gidan jiya dan Allah a sassauta mu su....." " Ni ma haka ne, dan har ruwa na fita na ɗibo da safe, ban masan ya ta yi ba ta dai ce min ba ta iya girki ba, nima ban iya ba amma haka na mana Indomie sai dai me sai da ya koma kaman fate." Sai da Rash ya yi dariya, abin da ya kan yi wiya kaga ya na dariya sai murmushi. " Skiddo kwanda kai, Ni ai fito wa na yi na bar ta da bread." Faɗin Spider, sai Rash ya kallesu ya ce " Taimako na za kuyi ina son na inganta rayuwansu cikin aminci, duk da ina ƙaunar su amma ina son su san talauci sosai, daga yau abincin gargajiya kawai za kuce kuna so kuma kubasu umarnin su yi, ban san ku nuna mu su tausayawa domin ganin tausayanku ba zai jijiga su ba, wata uku kawai na basu kafin nan ku kanku za kuji daɗin ha ka, matsalan Fancy amma ina son ita na tura mata ɓoyayyen guard, dan nasan wannan gidan akwai matsala dan Chul akwai shi da rigo." Daga haka suka dan tattauna ka ɗan sannan suka wuce, tare suka je ra har ko wanne su ya shiga na sa gidan da zullumi ya suke. END. https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 44 *************** *************** " Ya Adam a haka zan rayu? wallahi ka sauya min, ina son rayuwan hutu da jin daɗi, friends di na sai zuwa gulma suke yi, gaskiya da sake." Kandy ta kai aya tana kallon sa da ke zaune a gefanta sannan ya ce. "I'm sorry Sweet-kandy komai zai wuce amma ki de na ɗaukan kanki a wata, yanzu nan gidan mijinki ne can kuma na Pazars ne, da wannan gidan za ki yi tinƙawo da alfaha...." " Allah ya tsare ni Yaa Adamsi, ko abinci na ka sa ci a gidan nan, gashi kasan ban iya girki ba kuma sai da na tambaye ka, i need ordinary maid idan minyi aure." " Shike nan zan sa mo miki amma kibari ki kwana biyu tukun." " Hmmmmm Allah ka dube ni, da rayuwa......" " Khadijah!." ya daka mata tsawa sannan ya ci gaba da ce wa "Menene ai bin gidan nan?, Na gaji da rarrashin, Babban yaya zan kira na fa......" Jin ya ce Babban yaya ya sa hantar cikin ta ka ɗa. " Ya Adam ni ban ce ba, amma ya zan yi wai dan Allah ka dubi....." Janyo ta jikinsa ya yi yana lallaɓan ta, abin ka da uwar sangarta sai faman sauke ajiyan zuciya ta ke kaman ya buge ta. " Kandy ni talaka ne, ban da kuɗi banda wadata, amma ina son ki duk da kinfi ƙarfina tin da gashi kin raina in da na kawo ki." ya faɗa ya na haɗawa da murmushi dan ya san ta na son sa sosai. " Kai ma ka san ina son ka, zan zauna a haka kuma zan yi ma biyayya in ha Allah." Sai ya ɗaga mata kai, sannan ya janyo ledan da ya shigo da shi, hannunsa na kewaye da ita, a haka ya buɗe sannan ya ciro abu ya na ce wa " Dubi abin da na si yo ma na." Ta ɗago tana kallon abin da ke hannunsa, Power bank ta gani 50000ml, kuma full charge. " Kin ga na siya ma na duk da ban gama haɗa kuɗin sa ba, so na ke mudinga bin komai a natse, da na samu kuɗi nan ga ba zan sa ma na nepa, sai in miki bohold daga nan sai sola kinji, da ba bi sa ni gidan gaba ɗaya zamu sauya ma." Ta ra sa me za ta ce, shin farin ciki zata yi ko ihu za ta sa, wayanta da da ma ya kusa ɗaukewa ta jona, sannan suka je kitchen, kwai suka soya suna hira sannan ya suka ci da bread din safe, da gyar ya samu ta ci abinci shima ya ci kaɗan dan a ƙoshe ya ke, hira suka ta ɓa da shan soyayya sannan suka yi barci. *************** *************** Shi ma Skiddo ko da ya shiga, kuka ya ga tana yi abin har dariya ya ba sa, da yake Beasty akwai ɗan tsafta kitchen din ta da bayin ta na ciki, duk ta wanke, ta gyara harda sa turare ta ba ɗe, ko ina, ga kitchen ɗin an zuba uban kayan abinci, da gyar ta samu tayi jollof spaghetti na manja dan searching ta yi shi ne ta bi komai, ba laifi a bakin ta yi daɗi amma a ido sai haƙuri ɗan ta caɓe sosai. " Queen kukan me kike yi ne.?" "A ce ina Amarya amma ka fice tin safe sai yanzu, nai ta kiran number ka ba ta shiga, ga dare ya yi haka na zauna a tsakar gida sai na ga wata mage ta akan katanga shine na shigo....." " Wayyo Queen ki ya ƙuri kin ji, ba zan sa ke da ɗe wa ba. Yanzu dai ga Power bank sai kidinga charge tin da nan ba'a wani samun huta." amsa ta yi tana mai godiya dan ita sam ba ta da raini kaman yayarta Hauwa'u, amma akwai bincike da kure mutum, a palourn ya zauna ita ma haka ta zauna ta na aje flask ɗaya, ya san ba ta iya girki ba amma be son kwasale ta ya ce. " Amarya da girki wa ya sa ki? Fisabilillah." " To tin da Ango ya fice ai dole na samar ma kaina abin da zan ci." a ƙoshe ya ke amma ya amsa taliyan wacce ke ta tiriri, a kallo ɗaya ya ga jakwalkwalon ta, murmushi ya yi har ze aji ya ta ce. " Ban ga ne ba, ai na san ba ka so na shi yasa ba za ka ci abinci na ba." Sai ta sa kuka saurin ɗauka ya yi ya ɗaura kan table ya na jujjuya fork ɗin hannun sa, share hawayen ta yi ta zuna akan table din sannan ta amsa plate ɗin " Kulle idanun ka." Yba musu ya kulle sai ta kai abincin bakinsa ai kam a natse ya amsa yana taunawa a hankali, sai ya ji ya yi ɗanɗano a baki, ai kuwa a haka har ya cinye plate din, leather water ya sha. "Wato girki queen a ido subuhanallah, amma a ba ki Alhamdulillah." Murmushi ta yi sai aka ka wo nepa, take unguwar aka hau Nepa! . sai suka kalla juna suka kwashe da dariya. *********** ************ Zau ne su ke kowa rai a ɓa ce, dan tin da ya shigo Beauty ke neman maganan sa dan suyi dambe har ɗammara ta ci abin ta, wai ita akan me ye zai kawota gida kaman kejin dabbobi, yadda ya fita haka ya dawo ya ga gidan, sai ma tsakar gida da ya ci uban dau ɗa, shi kansa zai so ta yi hankali kafin nan da wata ukun, be bi ye mata ba ya yi kwanciyarsa, ita kam ko Power bank din daya ba ta anan ta ajiye ta na ta faman huci, chinchin din da su Baby su ka kawo mata shine ta ci ta ƙoshi abinta. ganin zaman ban za ta ke ya sa ya shiga ɗakin ya kwanta gefansa, har barci ya ɗauke ta. END [7/5, 14:19] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 45. After eight days ***************** ***************** ROYAL HOSPITAL WHITECHAPEL, RD. LONDON E1, 1FR, UK. ______ "Doctor A.A, you can go now. Everything about your discharge has been completed." Wani bature ya faɗa yana miƙa ma AA file, amsa ya yi ya mai godiya sannan ya kalla ƙofan toilet din da yaji alaman buɗewa, a hankali ta futo daga ciki tana goge fuskanta da alaman wankewa ta yi, kallon kallo suke yi da juna sai kuma ta sakar mai murmushi ta ke yaji hankalin shi ya kwanta, za ma ta yi gefan gadon ta na ce wa. " Na shirya za mu iya wuce wa." yaune karo na uku da ya ji muryanta mai daɗi, kallonta take yi yadda y aga duk ta rame saboda watannin data yi cikin doguwar suma, a ƙalla wata 8 da sati biyu kenan, kuma Alhamdulillah ta dawo nomal sai dai komai na brain dinta ya goge, fita suka yi cikin natsuwa suka shiga hotel din nan dan dama ya kwashe komai na su ya mai da, Room F13. suka shiga, za ma ta yi a kan gado tana bin ko ina na bedroom din da kallo dan komai sabo ne a idanunta, hatta fararen fatan da suke yawo a ko ina na garin. " Ba ra na sa mo mana abinci" kai kawai ta ɗaga mai ya fice, tafiya yake yi cikin farin ciki mara misaltawa ya rasa da me zai kira da wannan al'amarin, tina abin da doctor Alex ya ce mai ya yi 'Idan har kana so ta tina komai na rayuwarta ta baya dole ta dinga ganin manya manyan abubuwan da suka same ta na rayuwanta na ba ya, idan tana yawan gani komai za ta tina kaman mahaifarta, ko wani kalma da ta sa ba faɗa da ba ta labaran rayuwata da dai sauran su.' "Ina har abada ba zan bari ta tina ita wace ce ba." ya furta a fili yana shiga restaurant din hotel din. Kallon kanta take yi a mirro, budurwa doguwar kyakkyawa fara ƙal, mai zubin surar jiki dai dai wadaita. ji yake kaman ba ita ba, an ce mata komai na kanta ya goge sai ɗan abin da ba'a rasiaba, yanzu an ce brain dinta ta koma na yara dan empty take, sai wanda ta fara gani wai shine mijinta wanda ta ji ana ce mai Doctor AA. shigowan shi ya sa ta kai idanunta kansa, ya na da kyau fiye da misali, dogo wanda ya fita tsayi, gashi kaman zubin ƴan ƙasar nan, ga wannan baƙin gashin na sa sai shining ya ke, za ma ya yi yana miƙa mata abinci da yake yunwa take ji, amsa ta yi, sandwich ne ji ta yi ɗanɗano be ma ta ba amma haka ta ci dan yunwa sosai ta ke ji. *"Nigeria,"* ya amsa yana ɗago kai daga kallon screen ɗin wayarsa. *"Ni ma ina da 'yan uwa a can?"* *"A'a, ke ba ki da kowa sai ni."* *"Toh, I want to learn the language everyone here is speaking, ni ban iya sosai ba"* *"Just get better first, I’ll enroll you in school soon."* *"What is school?"* *"It’s a place where you’ll learn how to read and write."* *"Oh, so what did you say my name is?"* *"Airah." *" Meaning?." " Mai daraja ko wacce take da haske mai kyau." *"Okh and you, what’s your real name?"* *"A.A."* *"A.A? I don’t understand." Ya sauke numfashi, yana jin gajiya da tambayoyinta, sai ya ce: *"Abdullahi Anas. That’s enough questions for today, okay? We’ll continue tomorrow." Daga kai ta yi tana bitan duk abin da tattauna yanzu. **************** ******************** Air Force Base Tin asuba ta fita zuwa kitchen sai yanzu 10am ta kammala komai shine ta shiga dan ta huta, kwanciya ta yi dan jikinta duk ya yi tsami, babu laifi zuwa yanzu har ta fara sabawa, wahala sha take kaman me, kuma ba ta da ikon mu sa umarnin kowa a gidan, rayuwa take kaman ƴan aiki, dan har gyaran gidan ita ce, a da Dad ta sha yana son ta ne amma zuwa yanzu ta fahimci shima ba ya ƙaunarta, gashi M.d ba ya iya komai akan haka sai dai ya yi ta ba ta haƙuri kawai. Har zaman gidan ya ishe ta amma a duk lokacin da wasu suka zo gidan sai Maa ta yi ta nuna ma ta ƙaunarta, har ta kwammaci rayuwa irin ta su Kandy na talauci akan wannan rayuwan da take yi, dan har ɗa rama ta yi shuru ta yi tana ta wasiƙan jaki sai taji an banko ƙofar parlour na ta, ta san Maa ce dan haka da ƙyar ta miƙe ta fita, a parlour ta samet a tana haɗe fuskan kaman hadari, tsugunnawa ta yi ta ce. " Maa ga ni, me kike buƙata?." Kaman ba za ta ce komai ba sai ta ce. " Na ji ban sha'awan Rice and beans ne, ina son ɗan wake kaɗan sai custard da akara." " Ba ra na watsa ruwa sai na....." " Yunwa na na ke ji, dalla tashi." Ta ƙarasa cikin tsawa sai ga hawaye a idon Fancy ya gangaro, fita ta yi ta nufi kitchen tana shiga ta share hawayen tare da yin shu'umin murmushi ta na ce wa. " Wallahu kun gama mora ta daga yau sai dai ni na more ku, sannan zanga idan za ki iya cin abincin na wa." cikin sauri ta yi komai dama ba ta iyaba gashi ba ta yi niyya ba, tana gamawa ta kai daining sannan ta sanarma Maa, da yake yunwa take ji da gaske sai ta je ta zauna, sannan ta kalli komai, custard din yellow ne zar alaman be ji ruwan zafi ba kaman ƙullu ha ka yake duk da ta sanya milk amma be can za colour, akara din kuwa waken ko niƙuwa a blander be yi ba ya wani iri hakan nan, sai shi dan wanke wanda shi nomal ne amma ya yi mugun tauri, shuru ta yi ta rasa abin ce wa, wayanta ne ya fara ringing tana dubawa ta na new number WhatsApp voice call ne, accepting ta yi ta kai kunne ta, jin muryan auntan ta wanda tin da ya tafi be kira ba, a maimakon su gaisa ta haushi da faɗa, miƙewa ta yi ta dhige room din ta. Ganin haka Fancy ta wuce na ta ɗakin tana ai yana da Maa ta ce wani abu ta sun kwashi ƴan kallo. tina wayan da suka yi Babban yaya ta yi. (Kuka ta ke yi, ta faɗa mai komai, abin da ya ce ma ta shine ya faranta mata sosai * Fatima kar ki za ma shashasha ma na, ke fa mace ce na yadda da tarbiyyan da muka ba ki, ke kanki za ki iya gyara gidan auran ki, ki natsu za ki samu mafita*. A cikin kalaman sa ta ɗauki haske. ***** "Ban ga ne ba? ba za ka dawo ba ka ce?." Faɗin Maa ta na ɗan hu ci, " A'a zan dawo amma 1 week zan yi domin aiki ya main ya wa." " Ina yawan fa ɗa ma ka, da ka dawo nan ka fara aiki, menene amfanin asibitin ka, ga ma na ƙawata Maman Salma in baka son na ka." " No Maa kawai kibar maganan. Next week zan zo du ba ku." " Toh naji ya maganar Salma?." tana fatan ya ce ya amince sai dai ya ce. " Maa kibar maganan salma sam yarinyar ba ta min ba." " Kamar ya Autaa....." Ƙit ya kashe wayan, ta bi kiran amma offline, tsaki ta ja tana jin ta ƙoshi ma ga ba ɗaya dan ba za ta iya sa komai a bakin ta ba. END. [7/5, 14:19] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 46. ******************** ******************** Malali Baban gida ne mai kyau dai dai, mota ce ta yi parking ta ke wata budurwa ta bayyana, ba duguwa ba ce can amma ba laifi tana da tsayi, skin din ta me duhu ne amma saboda shan gyara da hutu sai glowing yake yi, wando crazy tasa sai riga ƙarami me dogon hannu, ga uban attach wanda ya zubo a kafaɗarta, a kallo ɗaya za ka sha ba musulmai ba ce sai dai in kaji an kira ta dq SALMA. shiga gidan na su ta yi ta na aje jakkanta kan kujera tana cire hill shoes din ta, za ma ta yi kan kujera ta na latsa wayanta sannan ta kai kunne. "Jubby yaushe za ki dawo?." Ana ba ta amsa a cikin wayan ta katse tana ajiye wayan, sai ga ƴan mata biyu sun nufota suna mata barka da zuwa. "Aunty Salma me kuke buƙata.?" Duk da wacce ta ce ma Aunty ta girma salman sai ta ce " Ku je ban buƙatan komai a yanzu " Daga haka suka bar gurin cikin sauri sauri. tsaki ta ja tana nufa party din ta. tana shiga ta ba je kan makeken bed din ta ta hau bancin asara dan tin 5pm sai 9pm ta tashi, wanka ta yi sannan ta sanya kayan barci fitowa ta yi tana kallon Hubby wacce ta je zaune ta ja duba file. " Hubby kin dawo?." " Eh Salma tin ɗa zu,na leƙaki kina barci ai." " Okh Hubby, Dady ya shigo kuwa?." Wanda aka kira da Hubby ta ɗago fafaren idanunta wanda suke cikin farin glass, kallonta tilon ƴarta ta yi wanda ita ce komai na ta ta ce. " Ya dawo amma ya ɗan fita ne." " Hubby ina son wasu kuɗaɗe Please." Ta haɗa hannayenta na ba roƙan Hubby din, shuru ta yi tana mamakin kashe kuɗin Salam ko 1 week ba ta yi da tura mata 3 hundred thousand ba, ta rasa me ke kanta kwana biyun nan. " Me kika yi da kuɗin da na tura miki five days back?." " Hubby kawai in zan samu toh in babu na kira Dady na.' " Ba zan b ada ba." Tafada cikin haɗe fuska dan sam ba ta son yadda ƴar ta ta ke mata magana, " Ƴa ta na wa kike buƙata?." Da sauri ta kalli Dady wanda shugowansa kenan, da sauri ta nufesa kaman wata yarinya ta rungume, cikin ƙauna ta ce. " 100k ne fa kawai Dady." " Don't worry my only one daughter." " Sannu da zuwa Abu-salma." " Yauwa Ummu-salma." haka suke kiran junan su har wasu ma kance haka. " Me yasa kake ƙara san garta Salma ne?." " Kamar ya ɗan ta tambaya kuɗi, ni fa gaba ɗaya dukiya ta ƴa ta ce Salma Nura Askira." " Na sa ni amma kashe kuɗin ya yi yawa." ita dai Salma shuru kawai ta yi dan in dai kanta ne sun sa b jayayya. " Ki barta ta huta da kuɗin Baban ta, ban san ki na shiga abin da babu ruwan ki." System da files din ta, ta ɗauka ta wuce ɗakin ta a fusa ce. "Dady ban san kuna samun misunderstanding a tsakanin ku." " Hmmmm za ta sauka ai, oya check your phone." wayarta ƙiran iPhone 16 ta du ba, da sauri ta duba ganin 500k ya sa mata, fa sa ihun daɗi ta yi, tana rungumesa sannan ta shige part dinta da sauri, tana shiga ta ta kira ƴan team dinsu, ta sanar da su ta samu kuɗin. Daga haka ta yi kwanciyarta cikin nishaɗi. **** "Ban son kina shiga rayuwarta, ke doctor ce, ni ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa duk dukiyan mu ta Salma ce kawai,ki yi ƙoƙarin faranta mata." " Sam ka kasa fahimta ta shin ka san yanzu ƴan mata da samari wanda suke samun kuɗi shaye-shaye suke yi a ɓoye, sai ya ci yaro sai iyayen su ke sa ni, kafin ka ce wani abu ƴan hanji sun sa mu matsala ko wani abu haka." " Mun san ƴar mu ai." Daga haka ya shiga toilet ɗauke da towel, hawaye ne ma su zafi suka zu bo mata sannan tana ta furta 'Astagfirullah' a cikin ranta. ************** *************** KK GRA " Hajiya yau za muga ko da gaske kike yi akan za ki banban ce Hassana da Husaini." faɗin Husain (Yunus), " Ha ba na gane ku balle ma su." Take suka fito Hasty da Husty cikin shigan Abaya Black sunyi rolling da vail kaman hijab, su kansu Twins din sai dai suka ce ma sha Allah ganin yadda suka yi matuƙar kyau. dayake kullum sai Hajiya ta ce ai tana gane su. Abin da ko su Yunus da gyar suka fara banbance su. " Wannan ita ce Husaina sai ga Hassana." Ta nuna su, sai suka yi dariya, da ya ke muryan su da ɗan banbanci ita Husty ta na magana da slow sannan magana ɗaya biyu sai ta yi english, amma Hasty ba ta cika yi ba sai in ta je school ko suna wani hira haka, Husty ta ce " Wow Hajiya, ya kika ga ne cikin sauƙi ha ka?." " Ha ba aiku yara ne abu biyu na rige kuma da shi na ke ga ne ku." "Explain more..." a tare Yusuf da Yusuf suka faɗa hakan sai Hajiya ta ce. " Yadda kuke suka haka suke, Hassan ko ka yi murmushi ba ya amsan fuskanka haka Hassana take, fuskan ku be da fara'a me yawa, kuku ma yana amsan na ku fuskan wato murmushi." " Kaji baiwa malam...." Yunus ya faɗa fa sigan wasa sai Hasty ta ce. " Ba komai kwanda mu nuna mu manya ne a ko ina " Sai suka yi dariya sannan Husaina ta ce. " To Hajiya sai kuma ne ne kike me ne.?" " Uhmm, launin ku ya ɗan banbanta sannan giranku ma haka, shike nan." Hajiya ta kai nan tana kai colanut bakin ta. Zama suka yi duk kansu su na ta hira da cin abinci kwanin burgewa. Hajiya fatanta Allah ya basu ƴan bibbiyu su ma, dan har ranta take son Hassana da Hussaina saboda sun ba ta respect kaman mahaifiyar su. END [7/7, 18:34] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 47. ***************** ******************* "My Pretty SK, yanzu kin ga ki na daga ɗakinki za ki dinga komai da ya dan ganci binciken." Zaki ya faɗa yana kunna socket din da zai ba dukka na'urorin gurin huta, Sk da ke ɗauke da wani Flash ta jona ta na ce wa. " Haka ne, so now I need ......" Ta katse magana saboda ganin wani paper me ɗauke da kalmomi hudu na babban maƙiyin ta wanda take ne ma ruwa a jallo, dan shi ne sanadin rasa ƴan uwan ta 'Rash' shine ta rubuta ta na ta har haɗa sunaye ko zai fito da asalin sunan wannan mugun amma ta ka sa. "Pretty zuwa yamma na ke son ki haɗa komai da komai a kan list ɗin." Ɗaga kai kawai ta yi ta na ganin ai aikin ko 1hours ba za ta ɗauka ta na yi ba, tare suka kammala haɗa komai, anan ɗakin yana aiki tana feeding na sa breakfast, miƙewa ya yi ta mai rakiya har bakin get, da yake motan shi na Abuja ya tsara nan da sati ɗaya za su je tare da Pretty dan gaisheta ƴan uwan sa na can ɗin, da yake yanzu motan da yake amfani tsohon na Aliyu ne, shi yasa ya shiga gidan, safiya ce yawan cin ba su ta shi ba. Babban palourn ya shiga bayan jami'ai sun gaida shi. Babu kowa dama haka ya yi tsammani, za ma ya yi ya na son tina jiya wa ya ba key ɗin motan daya dawo duk da sai da Aliyu ya ce ya barshi amma yaƙi kuma be son ɗauko motan station ne. Shuru ya yi sai ya tina Aunty ya ba dan ita ya samu a compound ɗin jiya, ga time na ta tafiya dan yanzu 7:23am kuma ya na son ya yi wani muhimmin aiki ne kuma zai je coat akan kai wani me laifi. wayansa ya ciro kafin ya fara latsawa sai yaji Butter na gaida shi, ya amsawa ya yi da sakin fuska. " Fadila har an shirya school ɗin?." " Eh Uncle Zaki." Take Baby da Karis suma suka fito cikin shirin Uniform iri ɗaya, suma gaishe shi suka yi ya amsa yana mai kallon wayan sa sannan ya ce. " Fatan kunyi breakfast ko?." " Eh lunch za mu ida haɗawa mu sa a lunch back." Suna kawai nan suka shiga kitchen dan juye jollof spaghetti wanda yake kan huta. dan yanzu girki abin da zasu ci suke yi da kansu umarnin Babban yaya, tin basu iya komai ba amma da taimakon Baby wacce ke koyowa a gurin Ramlat. Butter ce ta zu ba mu su a babban flask, sai Karis ta farfasa boil eggs guda shida, a wani roba me huji-huji ta sanya, ita kam Baby snack ta ke zu ba wa a gefan basket da zasu tafi da shi, take suka ji horn na mota fitowa suka yi a lokacin har Zaki ya huce. Motan suka hau suka nufi school, a yanzu shirin Waec suke. *************** *************** Kallon ƙafarta ta yi wanda duk sun kumbura duk da duk bayan magrib suna za ga ye gidan ita fa Ramlat, duk ta yi duhu dama ba haske gareta ba, sannan ta yi wani ƙira amma kyaunta ƙaruwa ya yi. " Omry da kinji wani yana yi Please ki yi gaggawan faɗa mutanen gidan." Murmushi ta yi mai dan kullum abin da yake ce mata kenan idan ze fita. Tsugunnowa ya yi saitin tulelen cikin na ta sannan ya sunba ce shi, daga haka ya fice dan bayan ya ma ta addu'a. Yana fita ya haɗu da su Pazar M da Pazar R suma sun fito, mota ɗaya suka hau direct sai office anan kuma kowa ya huce na sa ɓangaren. Tin daga ne sa ya hango Askira wato sabon sactary dinsa, a tare suka ƙarasa babban office din Gomna, Aliyu na za ma ya ce. " Ga wannan list din na ga ma tsarashi kuma yadda na ke so komai ya tafi a tsare." Askira ya amsa yana karanta paper sannan ya ce. " Sir an gama." Da ga haka ya fice abin sa, Aliyu miƙewa ya yi yana kallon haraban cikin compound ɗin wanda tin da ya shigo ya hangi wasu mata su uku daga gefe sun rakuɓe, ganin ɗaya daga cikin jami'an sa ya nufeta yana koransu irin na rashin imani haka, Telephone ya janyo yana dan na kiran number Askira, bugu biyu ya ɗauka yana mai miƙo gaisuwa. " Ina da ga be ne yanzu haka, ina hange wasu mata su uku, a turosu office di na." " Sir ba wajanka suka zo ba, ɗaya daga cikin su ce take son ganin yaron ta dan ɗaya ne daga cikin jami'an tsaron gidan nan, amma ba mu gan shi ba, an tambaya abokansa su ka ce tin shekaran jiya be zo ba." Askira ya kai nan yana mai fatan Aliyu ya yadda, sai dai me kafin ya gama firar zuciya ya ji ya ce. " Turo su." Daga haka ya katse kiran yana kallon su, dan har sun fara tafiya, baya jin wannan ne ya kawo su, domin last week ma yaga fuskan ɗaya ta zo ta huni a filin gurin. Ganin an kira me korasu ya sa ya koma ya zauna yana ɗauka home phone na sa tare da kiran Omry, amma hatta katse ba ta ɗauka ba, sai a kira na biyu ta ɗauka da sallama ya amsa yana mai sakin fuska. " Maman Babyna." " Na"am Baban baby, ya aikin toh?." " Alhamdulillah, ya jikin na ki?." " Lau mu ke, Ramlat na miƙo gaisuwa." " Ina amsawa." "Za ta ji, ita ma Sk haka dan gata gefe na." " Ma sha Allah ki ce nan aka zo hira yau, ba ra zan kira ki bye take care please dear." kafin ta amsa ya ba da umarnin shigowa, ya aje kiran sannan ya kalli wanda ya kawo mata ukun ya yi mai nuni da ya fice, gurin za ma ya nuna musu duk suka zauna suna mai jin daɗin yau dai sun ga His Excellency Aliyu Haidar. Duk da su ne manya amma su suka gaishe sa sai ya mai da mu su gaisuwa. " Ina son na ji lafiya tin ba yau ba na ke ganinku a gurin nan." " Yallaɓai wata ɗaya kenan kullum sai mun zo amma haka muke koma wa watara su koremu wata rana su haɗa da duka, amma haka muke dawowa dan san ganin ka." ɗaya takai nan sannan ta tsakiyan ta ce. " Mu ƴan tsaunin da wa ne, wanda ke cikin Rigasa, muna cikin mawiyacin hali, muna neman taimakon ka Yallaɓai." sayi ta hau kuka, gyara za ma ya yi yana ce wa. " Karku damu inajin ku." " Yallaɓai ka san damuna ta kama ƙasa, mun yi shuke-shuke a gaba ɗaya filayenmu, wata biyu baya, wasu jami'ai da manyan mutane suka kawo mana ziyara, bayan sunyi mana kyaututtuka sai babban cikinsu ya ce mana, ya na so mubar tsakanin dawa domin ze gina Company agurin ne." Takai nan tana nun fasawa sannan ta da sa " ya ce ya bamu sati biyu, da muka yi gardama akan ba za mu bari ba saboda nan ne duniyar mu kuma munyi shuka, take ya sa wani ya babbaka gaba ɗaya gonan na mu." Sai kuka ya kwace mata, sannan ɗaya ita ma ta da sa da ce wa. " Abu kaman a Film, Yallaɓai duk wanda ya ƙalu balan ce su to ka sh eshi su ake yi, rayuwa acan yana bamu tsoro." sai da ya sauke kwaron numfashi sannan ya ce. "Yanzu ku faɗamin sunan unguwan, zan so na bincika amma kun tuntuɓa shugaban da ke wakiltan arean na ku?." " Yallaɓai har dashi a cikinsu, sannan da wasu manyan Mutane." Shuru ya ratsa sanann ya amsa location dinsu, kuɗi ya basu me ya wa da cewan gobe zai shigo ko ya turo, Huce wa suka yi suna fatan da su samu sauyi a rayuwansu. rufe idanuwan shi ya yi yana jin babu daɗi. END. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [7/8, 06:07] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 48 **************** ***************** Opposite ROYAL HOSPITAL WHITECHAPEL, RD. LONDON E1, 1FR, UK. Taxi ce ta yi parking a bakin baban hotel din, fitowa ta yi daga ciki ta na mai biyan me Taxi kuɗin sa, ya amsa ya wuce, cikin hotel din ta shiga direct room din su ta shiga, wanka ta yi sannan ta yi sallah, addu'oi ta shi ga yi yadda A.A ya koya mata, tana gamawa ta miƙa ta kunna TV tana mai kallon wani Nigeria Film Rich mom and poor mom. tana jin wayarta ta kira sallan magrib, a cikin app din V-muslim dan ba masjeed a kusa da su. Bayan ta idar ta ɗauki sabuwar wayanta ƙiran Galaxy A05, data ta kunna ta hau internet dan yi assignment din ta. tana cikin yi aka buɗo ƙofan, A.A ne ya shiga bakinsa ɗauke da sallama, amsawa ta yi tana mai miƙewa ta nufesa da murmushi, rungumesa ta yi yadda suka sa ba, sai a lokacin ya buɗe bakin sa ya ce. " Fatan kina lafiya?." "I'm fine Monceur." sai ya riƙon hannuta suka ƙasara cikin palourn, zama suka yi, ta taimaka mai gurin cire safan ƙafan sa, tare suka shiga bedroom sai ta fito bayan ya shiga toilet danyin wanka, da yake ba irin ƙananun hotel ba ne, wannan ya na da komai a ciki, mutum ba ma zai ce hotel ba ne in dai kana cikin room. Bayan ya fito tare suka yi sallan isha'i sannan mai kawo mu su abinci ta kawo, ci suka yi suna hira kwanin sha'awa, ɗago idanunta ta yi ta kalli AA, ƙura mai idanunta ta yi tana ƙare mai kallo, kyakkyawa ne sosai, duk da be da yawan fara'a da surutu, gashi iya rayuwarta da shi taga ya na fa halaye na gari. taimaka mata ya yi suka yi sauran assignment dinta dan ya sa ta a wa ta makaranta anan din, ba University ba ne kawai school ne akayi dan ƙarin ilimi, kuma Alhamdulillah dan daga shigarta ta kware da English kuma irin na UK. Dan kafin suyi hausa yanzu su kan ju ma. Sai bayan da suka kwanta a bed ya ke mata albishir da ce wa nan da 1 month za su koma Nigeria ta ga familyn shi kuma ba zasu dawo UK ba. ita ce ta fara barci wanda kanta ta ɗaura kan ƙirjinsa, shi kuma yana kallo fuskarta, a hankali ya za me daga gadon, miƙewa ya yi, ya kunna globe take madaidaicin haske ya gauraya bedroom din, mirrow ne daga gefansa tsayawa ya yi yana ƙare ma kansa kallo, ji yake tamkar ba shi ba, wai A.A shine ya faɗa soyayya, ya yi aure ba tare da sanin kowa ba, rayuwan sa a yanzu ya mugun sauya, kaman ba shine ke rayuwa cikin ɓata garin yara ba, kaman ba shine shagalan duniya ya sa be ɗaukan mutane da daraja, kaman ba shine me shan abin da addininsa ya yi hani ba wato Alcohol, kaman ba shine ya yi sanadiyyan mutuwan mutane da yawa ba, amma tin da ga ranan da Airah ta shiga rayuwarsa duk ya sauya, ta mai dashin kamilin mutum mai yawan bauta ba tare da sanin ita Airan ce ta can za shi da soyayya ta ba. A yanzu abu ɗaya yak e tsoro shine idan ƙwaƙwalwan ta ya dawo, mai yuwa ta na da saurayi ko aure..... "Inaaaa" ya yi saurin katse zuciyar sa da wannan tunanin, yasan shi ya fara saninta a matsayin mace, yana fatan da ta samu ƙaruwar ciki ta haihu kafin komai na kwakwalwanta ya dawo........... END. [7/8, 06:07] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 49 ***************** ************** Air Force Base "Maa wai dan Allah yaushe za mu je gun malamin nan, ya ka mata tin yanzu mu san abin yi, daga tafiya ta wai ya yi aure, Maa a gaskiya ko wan can ta fita na shiga ko naje a matsayin kishiyar ta." Faɗin Hafsat tana kallon Maa, sai Maa ta ce. " Kar ki da mu Hafsat, ba ra gobe ta yi za muje da rana, ni kaina ina son na ga duk kan ku kunyi aure, ke Halima wai har yanzu baki gama tsara wannan yaron da ki ka ce kin so?." "Maa yaron ya ƙi bani hankalinsa, gashi a yanzu ba ya Kaduna ma, na ji an ce yaje Bauchi dan can ne family house na su ya ke." " To abin da zai faru dukka mu ukun zamu je muji me Malam Bulala zai ce." shuru ya ratsa parlour, sai murmushi ne ke sauka akan fuskan Hafsat wacce take ji kaman har ta auri saurayin na ta ne wanda take son sa, ji take kaman wannan shine auranta na farko ma, dan ma wan can 5month kawai suka rabu da shi. "Yunwa na ke ji sosai fa." faɗin Halima sai Hafsat da ke latsa waya ita ma ta ce. " 9:45am amma ƴar iskan can ta ka sa kammala breakfast." kafin Maa ta ce wani abu sai Fatima ta fito daga cikin kitchen ɗauke da plate a hannu ɗaya sannan ɗayan hannun tana riƙe da waya ta na chart da ƴan uwanta wanda suka haɗu a group dinsu, hira suke yi kwanin jin daɗi, dan a yanzu har zuciyoyin su sun salula akan maganan talauci dan sun yi haƙuri su kuma sun falwala ma Allah, gashi ita Fancy da ke cikin dukiya amma a ban za, sannan har Ramlat sun kira sun ba ta haƙuri kuma ta haƙura, Beauty ce ta rubuto 'Fancy ki dai bi a hankali, na san ki wani lokacin ba kya aiki da lissafi ba ki san mai ze je ya dawowa' kafin ta fara typing har Kandy ta turo sticker na tinani, murmushi ta sa ki sai taji Maa na magana ta na ce wa. "Ke wai ba ki da hankali ne ace goma saura baki kammala breakfast ba dan ma yau Sunday." hatta hau step 1 sai ta dawo ba ya ta ce. " I'm sorry Maa, wallahu tin ɗazu na kammala ya na kitchen....." " Uban wa zai kawo kan dining ɗin?." Faɗin Hafsah ta katse Fancy ta ce. "Duk uban da ke jin yunwa, mtwwws." ta ja tsaki tare da haurewa sama, tana jin Halima ta fara masifa ta banko ƙofan ɗakin ta, Indomie da fry egg ne ta haɗa ma kanta, ci take sunata hira abin su. A parlour kuwa Maa cikin fusata ta da Katar da Halima wacce ke ƙoƙarin bin Fancy. " Hmmm Halima bar ta, mu karya sai mu yi mata hukunci." daga haka Hafsat ta shiga kitchen dan fito da abincin da suka umarci ta yi, da mamaki ta ƙarasa ciki ganin babu alaman an yi wani girke-girke a ciki, dan ita wainar flawer da tea ta ce ta na so, ita kuma Halima yam, egg and pepper suop and bread sai Maa custard da Bons. da sauri ta koma palourn ta kirasu, a tare suka shiga kitchen wanda babu komai a gurin dan sun sha za su zo suga kulolin abincin, babban tukunya suka gani a gefan gas, halima ta buɗe sai sukaga Macronnie fari, sannan gefansa soyayyen oil ne. in ran su ya yi dubu ya ɓa ci. su ukun suka je bakin ƙofar ta suka fara Knocking, ta na jin su sai da ta kammala cin tukun ta miƙe tana vioce da ce wa "Jama'a sun iso bara na ji dasu ina zuwa." Daga haka ta a je wayan tana buɗe ƙofan, ko a fuskokin su ta san sun shaƙa kafin su yi magana ta ce. "Yaji ku ke ne ma?." "Barkono mu ke ne ma." cewan Halima tana ta muzurai, sai a lokacin Maa ta buɗe bakinta ta fara magana cikin ɓacin rai. "Wato ke gaki mara kunya, mu na zaman jiran breakfast ashe kina zaune a kitchen ɗin dan hulaƙan ci, ma za ki fito ki koma, na biki 30mnt da ki kammala komai ko ranki in ya yi dubu wallahi sai ya ɓa ci." " Maa wai ya kike mata magana a hankali ne, kyen shi mufara ma ta shegen duka tukun." ce wan Hafsat, sai Fancty ta saki shu'umin murmushi ta na ce wa. " To ai ni in ba ku sa ni ba ku sa ni, da ne na girkin gandun, na san ki na da hannu Bismillah ko wa ya shiga ya koya, balle ke Hafsat maybe shiyasa aka sako ki, baki iya girki ba. "Hafsah da ranta ya kuma ɓaci ta janyo Fancy wacce ke tsaye ko ge zau ba ta yi ba, hannunta ta ɗaga da niyyan ta mareta sai Fancy ta rige hannun ta na ce wa. " Kul Hafsat, wallahi karki so ma, kaf cikin ku babu mai buguna ya zauna lafiya, banza kawai." Take Halima ta matso dan su yi mata duka sai Maa ta dakatar da su da ce wa. " Karku duketa, muje mujira M.d daya ajiye ta, yau ta sa ni a gidan ubanta za ta kwana." " Bara na je na fara haɗa kaya na, Allah ya sa ya dawo da wuri." daga ha ka Fancy ta koma ɗakinta tare da banko ƙofa, tsaki ta ja ta na ce wa "Uban wa ke tsoron saki.", za ma ta yi ta ko ma koma online suka dasa hira da cewan gobe dukkansu za su zo gidan na ta. ---------- "Maa wai meyasa ba ki bari munyi mata shegen du ka ba?." " Halima ke yarin yace, tin da Maa ta hana akwai abin da take shirin aikatawa ne." " Shi yasa ba na wasu abubuwan a gaban Halima saboda har yanzu ke yarin ya ce, kubari gobe ta yi kusha kallo, ko in ce anjima." "Yanzu Maa ya zanyi? yunwa nake ji." Halima ta ƙarasa cikin ɗan shaƙwaɓa sai Maa ta ba Hafsat umarni da ta yi musu order, cikin jin daɗi ta yi order din amma sai nan da 20mnt za su kawo. " Gobe za muje Malali bayan min fara zuwa gidan Malam Bulala." "To Maa." suka amsa a tare, Halima wacce tafi kowa jin daɗi, ta tashi ta shiga bedroom din ta, wayar ta ta ciro ta kira numbern Salma, budu biyu Salma ta ɗauka cikin magagin barci sai Halima ta zauna a dressing mirrow ta na mai ce wa. " Salma gobe za mu zo, kin ga ba wani wahalan ki yi raping kwayoyin nan dan ba Maa, ki dai tanadar min da ya wa kawai, dan kwana biyun nan ban yi charji ba ji nake kaman ba ni ba." Daga cikin wayan Salma ta ce. "Ƙawata kenan, ba ki da matsala, akwai story amma sai kin zo." "Okh kina barci ban san na dame ki, sai kin ganmu gobe din." "Okh Haleemzee." Daga haka ta yanke kiran tana shigewa toilet danyin wanka. End. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [7/8, 18:37] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 50. ***************** ***************** Unguwan mai dabino ___________ Ranta a haɗe take kallon sa shi kuwa ko ajikin sa, hannu ya sa ya amsa wayan sa a hannunta sannan ya ce. " Madam ba zan kai dare ba na yi alƙawarin." " Ba wani amma ce min ka yi ai ba za ka ko ina ba, shine ka shirya wai za ka fita ." " Sorry Sweetie, My Sweet Kandy ta, kiran Babban yaya ne shi yasa." " Okh, karka manta da fura da nono irin na jiya." " Allah ya kawo kuɗin, zan siya mi ki, kar ki yi girkin dare da ni." hannunsa ta sa ki dan sun kai ƙofa in da zai fita, a hankali ta ce " Me yasa kar na yi dai?, Ba ya yin daɗi koh?." "Haba ai da ne baki iya ba amma yanzu kin kware ai, ba Maman zul-yadain na koya miki ba." "Uhmm yanzu su snacks za mu fara ma." " Kandy ki fara kwarewa a jollof dai." murmushi suka yi ma juna sannan suka rabu, maimakon ta kwanta kaman yadda ta sa ba, sai ta hau gyaran ko ina sannan ta kwanta tana jiran Maman Zul-yadain. ************* ************ "Ka manta wannan." faɗin Beauty tana miƙa ma Skiddo wanda ya ke amsa waya kuma ya na tsaye dan amsan jakkansa ta baya. amsa ya yi sannan ya sauƙe wayan daga kunne ya ce. " My Haulat ba ra na je in kinga ban kira ki ba to kiyi girki amma in na sa mu da ma zan siyo mana." " Toh Allah ya tsare, Please take care of yourself to me." Murmushi ya sa ki mai sanyi sannan ya fita daga gidan, har za ta shiga ɗaki sai ta fasa ta shiga kitchen, soya doya ta fara yi wanda zata yi breakfast, sai masu ɗiban ruwa suka shigo, cikin da ra ha ta musu iso, dan a yanzu ba ta damuwa, rayuwa ta ke ta riƙe Allah kawai da auranta. " Maman takwara, idan takwara ta dawo makaranta dan Allah ta zo na aika ta siyan kayan miya." Faɗin Hauwa'u tana fito da wanke-wanke tsakar gidan daga gefe guda, Matar da ta yi ma magana ta ce " To shike nan, za ta zo Allah yasa karta tsaya wasa idan an tashi." "To Ameen dan takwaran akwai son wasa kaman me." suka yi dariya,a haka har ta gama ɗiban ruwan, ta ɗi ba na ƙarshe kenan sai Beauty ta ɗiban mata soyayyen doya ta sa mata a leda ta ba ta, ta amsa da godiya tana hucewa har ranta take jin daɗin mu'amala da Hauwa'u dan akwai kyauta, gashi ba ta da rowa, ta dai san ta sauya ba yadda aka kawo ta ba dan a lokacin ko kallan su ba ta yi, sai ta kulle gidan ta hana ɗiban ruwan, amma daga baya sai ta can za, ta lura in dai ta san mutum ne take sakin jiki da shi.. ********************* ********************* __________ "NEPAAAAAA." Gaba ɗaya unguwan ta dauka dan an kawo hutan lantarki, da gyar ta buɗe idonta dan wani mugun barci ne ya ɗauke ta, ganin hutan lantarki yasa ta tashi t ajona wayan ta da power bank, sannan ta fita parlour ganin Almajirin ta na zaune daga bakin get din gidan ta ce. " Shazali yaushe ka zo?." " Aunty tin ɗa zu, na gama ɗiban ruwan ai." " Okh yanzu ka je gidan yayata ka ce ta ba ta power bank na yi ma ta charji." "To." Shazali mai kimanin shekara 11 ya tafi dan zuwa gidan Beauty, ko da yaje ya gaida ta, ta amsa cikin sakin fuskan dan ta san Beasty ce ta aiko shi, saƙo ya faɗa ma ta sai ta ce. " ka ce mata na ba da a nan maƙota kawai, sannan ka ce mata gobe ne, kar ta yi halin na ta." Shazali ya amsa da "To.", sai da ta ba shi abinci ragowan na jiya ya ci sannan ya wuce, faɗa ma Beasty abin ta ce ya yi, sai ta yi murmushi tana ti na gobe shine zasu je gidan Fancy sannan halin ta shi ne barcin safe. END. *****𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊**** [7/9, 10:36] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 51 **************** ****************** __________________ "Yanzu duk kansu ne a nan." Zaki ya faɗa yana ɗa ga papers ɗin da ke kan desk, sai Sakeenat ta ɗago Idanun ta da ga kallon computer, wanda take operating cikin kwarewarta. "Eh su ne, yanzu abin da ka ke zargi ya tabbata a kan Rash." "Amma ya shiga hatsari sosai, dan babu wanda zai iya fahimtar abin da mu ka fahimta mu." " Haka ne amma zan tura mai secret sms." "Na ƙa gu na haɗu da shi." ya faɗa ya na koma wa kan sopa. "Ni kai na ina son ganin shi, ina son nasan wanene shi." Zuciyar ta ɗaya ta faɗa hakan ba tare da tasan maganan ya da ki zuciyar Zaki ba dan mutum ne shi me kishin gaske, sam ba ta lura da yanayin sa ya sauya ba sai da ta miƙe daga in da take ta kalle sa. "Baby what's wrong?." Ta tambaya ta na zama gyefan sa, be kula ta ba haka be kalle ta ba, aka karo na biyu ta da fashi tana kuma ce wa. "Lafiya?." Kafin ta ce wani abu ya sa hannunsa ya cire na ta hannun da ta dafa sa, Ita dai a iya sanin ta ba ta yi komai da zai sauya mood ɗin sa ba, miƙewa tsaye ya yi sai ya koma parlour, ganin haka sai ita ma ta bi bayan sa, zaune ya ke amma sai ti na kalaman ta yake yi. "Daga yau za ki bar wannan aikin na ki na bincike." Ya faɗa da kakkausar murya, sai ya dawo ainiyin Zaki na gurin aiki. " Baby ban gane ba? Wani aikin zan de na?." " Abin da na ce kenan." sai ya nufa ƙofan fita har ya buɗe ƙofan ya ji ta na ce wa. "9:10pm dare ya yi ina za ka je?." " Ni kaina ina so na gansa, ina son na san wanene, hmmmmm." abin da ya ce kenan ya banko ƙofan da uban ƙarfi bayan ya fita, murmushi ta sa ki dan ta fahimci in da zance ya dosa wato kishi ya motsa. miƙewa ta yi ta kunna T.V ta sanya wani shiri da ta ke bibiya a Star Life TV. ___________Ya na fita ya shiga giɗan su Aliyu, gaishe shi guard suka din ga yi ya na amsa wa har ya shiga main parlour, Hajiya, Momcy da Mom ne ke hira cikin ra ha abin su, gaishe su ya yi suka amsa sai sannan ya zauna a gefan Mom dan sunfi wasa da ita. " Ango Ango, idon ka ke nan ?." cewan Mom sai da ya sosa kan sa kafin ya ce. " Mom wani ango kuma, ai mun tsufa mu kam." " Tin da aka yi bikin nan sau biyu Amarya ta shigo ta gaishe mu fa, why ba ka barin ta ta shigo?." Hajiya ta kan nan tana kallon Zaki, kafin ya yi magana Momcy ta ce. "Ai da an yi mai magana sai ya ce tana aiki ne babu lokaci, wa ya mutu wa ya tashi." "A'a Momcy ba ha ka ba ne, amma gobe za ta zo In sha Allah." "Allah ya sa da gaske, yanzu ma mai ya hana ku zo tare?." Mom ta tambaya sai ya ce. "Ta yi barci ne." Sannan ya miƙe dan tambayoyi ne zasu yi ta mai kan an aiko su, hannu ya miƙa ma abokin sa wanda ya fito tare suka yi musabiha. " Ba ra mu shiga ciki." " Ashe gun aboki ka zo ba gaishe mu ba." " Mom a'a, yanzu zan dawo ai, zan duba Meerah an ce ba ta jin daɗi." Daga ha ka su ka shiga part din Aliyu, za ma suka yi a kan sopa sai Aliyu ya miƙe ya shiga kitchen bayan dan lokaci ya fito ɗauke da babban plate, ajiwa ya yi akan center table ya na ce wa. " Yau za ka ci girki na fa." "His Excellency da kan sa ya ke girki, wow." "To ya zanyi sai haƙuri ai Madam ba lafiya jiya sai da mu ka je asibiti amma Alhamdulillah." Kafin Zaki ya yi magana sai ga Ramkat ta fito, tafiya take da ƙyar saboda nauyin ciki, sanye take cikin hijab blue har ƙasa amma a kallo ɗaya za ka ga ne kumburan ta da tayi da duhu, sai da ta zauna da taimakon Aliyu, sannan Zaki ya yi mata ya jiki, ta amsawa ta yi ta na sakin murmushi wanda iya fuska ne kawai dan ba ta jin daɗin jikinta. "Haidar ka san zargin mu akan Rash gaskiya ne." Ramlat ta za ro ido ta ce " For real Zaki?." "I'm very sure." yadda Sakeenat ta faɗa mai haka ya zayyana mu su, shuru ya ratsa gurin sai Aliyu ya ya ce. "Ikon Allah, wane ne wannan Rash ɗin, ka ce ta tura mai saƙon sai mu jira mu ga abin da zai ce." " Ya dau babban kasada da rayuwan sa." "Allah ya sa mu da ce, yauwa Aliyu gobe sunday muna da meeting da president Bola Ahamed Tunubu a Abuja, zan bi flight amma dole na ɓa ta lokaci, sannan ban san zuwa na fiso na tura a ɓoye." Take ya ba Zaki labarin wa'inda suka zo ɗazu office din sa sai Zaki ya ce. "Allah ya kai mu zanje, dan gobe ina free " Daga haka suka dinga hira har Meerah ta shiga dan yin barci, sun jima ba su haɗu sunyi hira sai yau. " Kai wai har 11:10pm ya yi." Faɗin Aliyu yana duba wayan sa, sai a lokacin Zaki shi ma ya an kara duk da so ya ke ya yi dare sosai. "Bara na je, na bar ƴar muta ne a gida ita kaɗai." "Gaskiya kam duk da akwai get-man amma be ka ma ta ba." Da ga haka su ka jera har main parlour, sannan Zaki ya ce. "Ka ga koma abin ka, zan ɗan gai da Aunty kan na wuce." Daga nan kuma suka yi sallama ya koma part ɗin sa, main parlour ɗin babu kowa sai Aunty wacce ta fito daga part ɗin ta, a duk lokacin da ya ga Aunty cikin farin hijab sai ya ga sak Mahaifiyar su dan ita ma'abociyar farin hijab. "Auntynah, Mamanah." ya faɗa yana isa gaban ta, za ma suka yi a akan kujera ɗaya, sai ya ɗauka kan sa kan cinyarta ya na ce wa. " Ina kewan Mama." "Nima ha ka Asad." Ta ke kalman 'Asad' ya sa Ramlat ɗin sa ta faɗo ma sa duk da kullum ita ya ke gani a tare da Pretty Sk. " Allah ya gafarta mu su, Baba da Mama." sai ya yi murmushi. " Ameen ƙanina." Hira suka ɗan yi suna yi tana sosa mai gashin kan sa, a haka har Pazar Q ya fito daga part din su yana ce wa. " Daga ɗauko min drink sai na jiki shuru, ashe Zaki ne ya riƙe ki." " Ya Allah, I'm sorry Baban Baby wallahi na sha'afa ne." Ta faɗa tana so ta miƙe dan tini Zaki ya ɗaga kan sa daga cinyar ta. "No bar shi har na sha wancan ai." Ya zauna ya na kallon su sai kuma ya ce. "Sai na ga kaman Zaki yana so ya fiki kyau ne." " Uhmmm ai na fishi, dan har yanzu angon cin ne be sa ke shi." "Aunty ango kuma, kin dai san ko a ɗa na fiki kyau sosai balle yanzu, dan ma ban hutu kaman ke da hmmmmn, Ni bara na wuce ma " "A'a zauna abin ka ni na shige ba ra na je na kwata." Faɗin Pazar Q ya na miƙewa, sannan ya wuce, sai Aunty ta ce. " Kafi Mama kyau koh?" " Ni awa, Mama ta fini ma na." Ya yi saurin ba ta amsa sai ta saki murmushi sannan ta ce. "Kuma ka ce sak na ke da Mama, to ni ban fahimta ba?." "Aunty ɗan kama ne kawai ku ke yi." "Kai wai lafiya 12:04pm ka na nan?, dare ya yi sosai fa." " Ok bara na wuce, ai nasan tayi barci ti ni." Jin hiran su Baby ya sa suka kalli in da suka fito, ta ƙofan ɗakin Babban ya suka fito, gaishe shi suka yi ya amsa sai Aunty ta ce. "Sai yanzu ku ka ga ma karatun?." " Eh Aunty, ba ra mu shiga, good night." Faɗin Karis, sannan suka shiga part din su, Butter ce ta kashe globe bayan ko wacce ta hau bed ɗin ta, sai Karis ta ce. " Allah yasa gobe muji alheri akan JAM result." "To ameen, kin ga idan mun ci sai mu roƙa zamu je gidan Fancy idan Pazars za su bar mu." "Haka ne Allah ya kai mu, kin san karatun yau ya ta shi kai na." " Baby muna ɗaya nifa har kunya-kunya Aunty Ramlah na dinga ji." sai suka kwashe da dariya dan ti na yau fiƙihu suka yi sun sha dariya, da yake yanzu kullum suna part ɗin ta dan koyan karatu da girki, da Baby ce kawai ke zuwa daga ba ya su ma su ka fa ra zu wa, kuma suna matuƙar jin daɗi karatun balle na yau. ______ "Hadith ne duk da ya na da rauni, (Manzon Allah (S.A.W) ya ce: Miskini ya ce! Miskini ya ce!! Miskini ya!!!. Sai Sahabbai su ka ce : Wa man ya Rasulullah?. (wa ye). Sai Manzon Allah (s.a.w) ya ce: Almar'atul lati laisa laha zawjun, walau ka nat ganiyyatun minal maaa).. Baby wallahi aure akwai daraja sosai, marta ban matar aure da ban da na budurwa, ga Bonus na la da. Karima da ki ran kwaɗa kwalli ki sha turare, ke kin ƙure kwalliya, kin ya fa ƙaramin Vail kin fita, wallahi duk haram ne, babu kyau, amma ni kam, ko a yanzu ace na ran kwaɗa kwalli wa Babban yaya na sha turare, ke idan ma Swimming dress na yi, la zan samu sosai fa." Sai da suka kwashe da dariya, Ita kam ko a jikinta ta kuma ci gaba da misalai, wani su yi dariya, wani kuwa su yi murmushi. Barci ne ya ɗauke su dan sun gaji ba laifi. END Daga Sakeenat Abdullahi. [7/9, 19:51] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... ' *Page 52. A parlour kuwa, Zaki ne da Aunty suka yi sallama sannan ya koma gidansa. Ya saka key ya buɗe parlour ɗin, sai ya tarar da babu kowa, sai T.V da ke aiki. Ya kashe shi, yana addu’ar Allah yasa ba barci ta yi ba. Da yake a ɗakin shi suke kwana, sai ya fara shiga, amma bai ganta ba. Ya wuce ya yi wanka, bayan ya fito ya sanya PJmas. Ya shiga ɗakinta, sai ya hange ta kwance cikin bargo. Ya murmusa sannan ya zauna a bakin gadon. Ya so dai yazo ya ganta tana jiran sa ta ba shi haƙuri, amma sai yaga barci take sha. Shuru ya yi, sai yaji ta motsa. Ta rungume shi ta baya, bakin ta kusa da kunnensa tana ce wa: > “Bazan iya barci ba alhalin Babyna na fushi da ni. Fushin ka kan janyo min tsinuwan Allah da Mala'iku. Wallahi ba da wata manufa na faɗa ba. Kai ma ka sa ni, a duniyar nan banda wanda nake so sai kai. Kai kaɗai ne Zakin Zaku na, masoyi abin so na.” Har ransa ya ji daɗin wannan kalaman. Ya rike hannayenta yana ce wa: "Ba komai, kawai raina ne ya ɗan sosu. Please, ki rinka kula da kalamanki. Kinsan ni mai kishi ne.” > “Insha Allah, Baby. Kishi ai halal ne. Manzon Allah ya ce: *‘Wanda bai da kishi ba, ba zai shiga Aljanna ba.’* Sannan ina so ka janye kalmanka akan aikina, ka ji?.” > “Shike nan, ya wuce. Matata abar ƙauna ta.” Daga nan ta zagayo gaban sa. Kallon ta yake yi cikin ƙauna mara misali. Suka koma ɗakinsa, bayan sun zauna sai ta ce: > “Bari na kawo ma ka abinci nan.” > “A’a, Alhamdulillah, na ƙoshi,” ya faɗa. Sai ta dawo baya tana ce wa: > “A ina ka ci abinci?” > “Gurin Meerah.” > “To ni wallahi ban yadda ba! Ina jin yunwa, na ƙi cin komai ina jiranka. Amma shine... uhmm uhmmmm.” Ta faɗa tana kifa kanta a gado, ta fara kukan shaƙwaɓa. > “Ya-salam! Daga cewa na ƙoshi sai kuka? To ya ƙuri, My Pretty,” ya faɗa yana ɗaga ta daga kwanciya. Ya shiga rarrashinta har ta yi shuru. Ta ɗauko abincin, duk da yana ƙoshe, sai da ya ci don zaman lafiya. *********************** ****************** RASH _____________________Cikin wannan gidan na sa motoci guda uku su ka fito black suka ɗauki hanya har suka hau kan titi, motan gaba da ba ya dukka matasa ne masu sanye da kaya kala ɗaya, kuma ko wannen su a bayan rigan sa sunan mamallakin mai sanye da shine sai harafi ɗaya a cikin sunan RASH, wani A, wani H haka dai suke, Airport suka nufa gaba ɗaya su goma sha shida ne (16), privet jet suka hau ba su sauka a ko ina ba sai Abuja, suna sauka a airport motoci da yawa suke jiran su, ha wa suka yi sai wani babban gida suka nufa, motoci bakwai ne suka yi parking a haraban babban gidan fitowa suka yi wanda a cikin su har da Shuraim, shiga su kayi wasu kuma suka tsaya a compound ɗin, gidan sai ma sha Allah, komai ya haɗu, ga ɗakuna ma su masifar yawa, wani room su ka shiga wanda na'urori ne kawai a ciki nan suka je suka hau aiki a ciki, Rash kam zama ya yi a wani kujera ya fito da wayan sa yana kiran number Ramlat, bugu uku ta ɗauka, a hankali yaji sanyaryar muryan ta, ta cikin wayan. " Ina kwana." sai da yaja fasali tukun ya ce. " Lafiya, kinga ban dawo ba koh?." " Uhm fatan Lafiya?, Ina ta kiran number ka baya shiga." " Ina wani babban aiki ne, kuma zuwa gobe zan gama daga nan zan dawo ainiyin Shuraim ɗinki." "Ma sha Allah, Allah ya taimaka, dama haka nake so da fata, dama ina so na ce muna asi......" "Asibiti koh" ya yi saurin katse ta sai ta yi murmushi sannan ta ce. " Hmmmm na manta ashe da Rash na ke magana." " Hmmmm mai a ka samu?." " Mace ce so pretty, mai kama da Haidar, yanzu ma ya wuce." " Ma sha Allah zan kira shi nasan yana ta ne mana a waya." dyaga haka suka kammala wayan, sai ya katse tare da kiran Aliyu, sai da kiran ya kusa katsewa tukun ya ɗauka, bayan sun gaisa Aliyu wanda shigan sa office kenan yana shirin wuce wa Abuja ya ce. " Ameen, na gode, na so Baby boy ne na sa sunanka amma girl ce, ka za ɓan min wani suna zan sa mata Baban yaya." " Karka damu ka sa ko wanne, idan kai ba ka da za ɓi, ai ita Meerah tana da shi." " To shike nan, Babban yaya inaji a jiki na kana cikin ƙoshin lafiya amma ban san yadda ka ke ni sa da ni, dan Allah kabar wannan aikin da ka ke yi ka dawo gida, haka Pazars kullum cikin complain suke, ace a week sau ɗaya kake kwana wani week ɗin ma ba ka kwana." " Shikenan zan duba." " Yauwa My big bro, na gode da aikin da kamin a kan wan can ƙauye, ina jin labarin nasan kai ne amma ban gane abu ɗaya ba, sun ce mutane da yawa cikin kakin sojoji, ka za ma soja ne ba mu sa ni ba?." " Zan kira ka anjima." Ya katse kiran yana sauraran abin da Skiddo ke ce wa. "Sir Rash done." Aje wayan ya yi yana nufan systems ɗin, bayan sec 10 yana kallon sunayen asibitocin da ke kan system ɗinta sai ya sa ki murmushi ya ce. " Ka haɗa dukkan su sannan da locations na su." "Okh Sir." Adam ya faɗa, koma wa ya yi ya zauna yana tina abin da ya faru jiya, da ya ke ya dasa na'ura a office ɗin Aliyu a haka yaji komai akan abin da ke damun su. kuma be ɓa ta lokaci ba dan take suka je suka magance komai, harta mutanan da suke da sa hannu ya yi maganin su. END [7/10, 14:39] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 53. ************** ************** SALMA CONSULTANT CLINIC Babban Hospital ne wanda ya ke da manya-manyan likitoci, ƙwararru masu sanin aikin su, ko daga haraban Asibitin za ka fahimci na masu kuɗi ne dan tsala-tsalan motoci ne ke cike da compound ɗin. akwai ma'aikata sosai, ga cleaners ta ko ina, sannan ko ina sai ƙamshim hypo yake. baban office ɗin shugaban asibitin wanda shima ya haɗu, wata ƙaramar nurse ce ta shiga cikin bayan ta yi Knowking kuma an ba ta umarnin daga na ciki. "Yes coming." gaishe da wance ke duba wasu files ta yi, sannan ta kuma magana ba tare da matar ta ce wani abu ba. " Doctor an kammala, za ki iya zuwa ki ganta." Da hannu ta yi mata alama sai ta wuce nurse ɗin, miƙewa matar ta yi tana gyara glass din idonta, ɓangaren masu Haihuwa ta nufa, Room 15 ta shiga, mata huɗu ne a ciki, gaisheta suka yi ta amsa cikin sakin fuska. " Ya jikin na ki?." ta tambaya wacce ke kwance a kan bed ɗin na marasa lafiya. " Doctor Alhamdulillah." " Allah ya raya." " Ameen, yaushe za kuyi discharge din mu?." Faɗin Ramlah wacce ke zaune gefan Aunty da Hajiya. "Tin da jikin da sauƙi zuwa an jima za mu sallame ku." Daga haka Doctor ta wuce sai Hajiya ta ce. " A kira su Mom da Momcy ace ba sai sun zo ba, tinda an juma za mu koma kawai." " Okh ba ra na faɗa musu." Aunty ta faɗa ta na kiran number Momcy. "Kema nan da watan gobe ko jibi za mu kawo ki." cewan Hajiya ta na duban Ramlah wacce ita ma cikin na ta ya fito sosai. " Na kammala haɗa ruwan." Tare suka kalli ƙofan restroom in da Sakeenat ta fito, miƙewa Meerah ta yi ta shiga bayin dan yin uzuri, dama ruwa aka sa Sakeenat ta haɗa mata, matsawa ta yi jin Baby ta ce. "Gaskiya babyn nan akwai kyau wallahi, ni dama ta ba ni." Dariya suka kwashe sai Aunty ta ce. " Ke ma sai ki ƙoƙar ta." " Barta ta sha abin wasa ne." Hajiya ta faɗa sai Ramlat ta ce. "An ya su Karima za su sa me mu kuwa, da a kira ace musu gobe sun zo gida kawai." " Haka ne, gobe su Hauwa'u sun zo zai fi musu." ************** ************** AIR FORCE BASE Dukkan su mutanan gidan ne zaune a parlour, shuru suka yi dan jira abin da M.D zai furta. "Maa ki yi mata duk hukuncin duk wanda ki ke so, amma banda maganar rabuwa." Bai jira ta ce komai ba ya fuce dan zuwa makaranta dan ya na da class 8:30, Maa wacce ranta ya yi mugun ɓaci, ta so tin jiya agama komai amma M.d be dawo da wuri ba. ga nin mijin na ta ya fice ya sa ta miƙe tsaye ta na ce wa. " Maa, aure na da M.D babu saki a ciki, watanni na yi a gidan nan amma akwai abubuwan da na fahimta akan ku." " Dan kinga ana miki da wasa, to wallahi ba tsoron ki muke ba." take Hafsat ta ruƙo hannun Fancy wacce ke tsaye, ko a ido an san tsaf Hafsat za ta ma Fancy duka du ba da yanayin jin su, amma abin ku da mai baki sai Fancy ta ce. " Hmmmmm, ina jin baki taɓa kwana a station ba, idan kin fasa taɓa ni, dalla sake ni." ta fizge hannun ta sannan ta kalli Maa ta ce. "Karr ku za ci kallon ku kawai na ke yi, nasan komai har da zuwa gurin bokan da za kuyi infact har ta M.d kin mai, na sa ni, kallon ku kawai na ke." daga haka ta haye sama ɗauke da flask din Breakfast ɗin ta, wanda yau ma sun sha za ta yi musu ne, har ta Dad haka ya fita dan shi sauri ya ke yi ne. "Ki kira Zulai ta dawo bakin aikin ta." faɗin Maa tana zama, maganar Fancy ta daki kan ta. " Maa ki ba ni umarni da na ci uban ta." " Mu ci dai Hafsat, ni wallahi so na ke mu gana mata azaba." "Ku yara ne, idan ba ka iya kama ɓarawo ba to shi ya ka ma ka, mu bi komai a hankali, yanzu ko Tea ne musha sai muje gurin Malam daga can muje Malali." basu suka fita ba sai 10:12am, direct giɗan Malam Bulala suka je, ba su jima ba ya sallame su, bayan ya basu magunguna guda uku, na farko wani ruwa ne wanda zata haɗa da turaren ta sai ta shafa, kar ta yi ma kowa magana sai shi wanda aka yi aikin a kansa, na biyu kuma da zaran sun fara magana sai ta kai mai abun sha sannan ta sanya wannan garin a cikin, na uku kwalli ne wanda Halima ce za ta sanya sannan ta tabbatar haɗa ido da wanda take so, take komai zai yi dai dai.. **************** **************** Bayan driver ya kai su asibiti direct ɗauko Beasty, Beauty da Kandy ya yi sannan suka nufa gidan Fancy, a mota suke hira kwanin sha'awa. Karis ce ta ce " Sisters, Aunty Ramlat akwai mutum ci, kun ga yadda muke kwasan ilimi a wajenta kuwa." " Ma sha Allah sai ku da ge, kun ga mu da muka raina ta sai Allah ya nuna mana ishara da auran talakawa." faɗin Beauty sai Baby ta ce. " In sha Allah." Ta window ta kalli motan da ke bin su, Bugatti ce white wanda take hange Husty ke driving sai Hasty gefan ta tana latsa waya, a ta baya kuwa Butter ke kwance ta na barci. Ko da suka isa babban get ɗin Air Force Base, suka tadda Fancy tsaye jikin wata babban mota wanda har yau ba ta san mai shi ba wai yana UK, ita dai ɗakin Maa ta shiga ta ɗauko key shine ta fito, bayan an gama bincike motocin suka shiga cikin babban unguwan. bayan sun yi parking a babban gidan suka shiga ciki. Su tara ne dukkan su sun sanya Black Abaya dan haɗa baki suka yi. sunyi kyau dukkan su, duk da irin muhallin da wasu ke rayuwa amma babu ƙarya jiki yana cin mai daɗi, lafiyayyen girki Fancy tayi musu suka ci suna ta santi, "Wai Fancy ke ki kai wannan girkin kuwa?." Butter ta tambayi Fatima sai ta yi murmushi ta ce. " Ai yanzu na za ma expect." "Mu ma yanzu mun dage da girki sosai." Cewan Kandy, hira suka sha sosai suna mai taya Fancy da addu'a akan Maa. " Result ya fito, yau da safe muka duba." Dukkan su hankalin su ya koma kan Karis wacce suke jira suji score din su. " Ni 187, Butter 180 sai Baby 210." Murna ne ya cika su ganin sun samu score mai kyau balle Baby. END. [7/10, 14:39] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 53. ************** ************** SALMA CONSULTANT CLINIC Babban Hospital ne wanda ya ke da manya-manyan likitoci, ƙwararru masu sanin aikin su, ko daga haraban Asibitin za ka fahimci na masu kuɗi ne dan tsala-tsalan motoci ne ke cike da compound ɗin. akwai ma'aikata sosai, ga cleaners ta ko ina, sannan ko ina sai ƙamshim hypo yake. baban office ɗin shugaban asibitin wanda shima ya haɗu, wata ƙaramar nurse ce ta shiga cikin bayan ta yi Knowking kuma an ba ta umarnin daga na ciki. "Yes coming." gaishe da wance ke duba wasu files ta yi, sannan ta kuma magana ba tare da matar ta ce wani abu ba. " Doctor an kammala, za ki iya zuwa ki ganta." Da hannu ta yi mata alama sai ta wuce nurse ɗin, miƙewa matar ta yi tana gyara glass din idonta, ɓangaren masu Haihuwa ta nufa, Room 15 ta shiga, mata huɗu ne a ciki, gaisheta suka yi ta amsa cikin sakin fuska. " Ya jikin na ki?." ta tambaya wacce ke kwance a kan bed ɗin na marasa lafiya. " Doctor Alhamdulillah." " Allah ya raya." " Ameen, yaushe za kuyi discharge din mu?." Faɗin Ramlah wacce ke zaune gefan Aunty da Hajiya. "Tin da jikin da sauƙi zuwa an jima za mu sallame ku." Daga haka Doctor ta wuce sai Hajiya ta ce. " A kira su Mom da Momcy ace ba sai sun zo ba, tinda an juma za mu koma kawai." " Okh ba ra na faɗa musu." Aunty ta faɗa ta na kiran number Momcy. "Kema nan da watan gobe ko jibi za mu kawo ki." cewan Hajiya ta na duban Ramlah wacce ita ma cikin na ta ya fito sosai. " Na kammala haɗa ruwan." Tare suka kalli ƙofan restroom in da Sakeenat ta fito, miƙewa Meerah ta yi ta shiga bayin dan yin uzuri, dama ruwa aka sa Sakeenat ta haɗa mata, matsawa ta yi jin Baby ta ce. "Gaskiya babyn nan akwai kyau wallahi, ni dama ta ba ni." Dariya suka kwashe sai Aunty ta ce. " Ke ma sai ki ƙoƙar ta." " Barta ta sha abin wasa ne." Hajiya ta faɗa sai Ramlat ta ce. "An ya su Karima za su sa me mu kuwa, da a kira ace musu gobe sun zo gida kawai." " Haka ne, gobe su Hauwa'u sun zo zai fi musu." ************** ************** AIR FORCE BASE Dukkan su mutanan gidan ne zaune a parlour, shuru suka yi dan jira abin da M.D zai furta. "Maa ki yi mata duk hukuncin duk wanda ki ke so, amma banda maganar rabuwa." Bai jira ta ce komai ba ya fuce dan zuwa makaranta dan ya na da class 8:30, Maa wacce ranta ya yi mugun ɓaci, ta so tin jiya agama komai amma M.d be dawo da wuri ba. ga nin mijin na ta ya fice ya sa ta miƙe tsaye ta na ce wa. " Maa, aure na da M.D babu saki a ciki, watanni na yi a gidan nan amma akwai abubuwan da na fahimta akan ku." " Dan kinga ana miki da wasa, to wallahi ba tsoron ki muke ba." take Hafsat ta ruƙo hannun Fancy wacce ke tsaye, ko a ido an san tsaf Hafsat za ta ma Fancy duka du ba da yanayin jin su, amma abin ku da mai baki sai Fancy ta ce. " Hmmmmm, ina jin baki taɓa kwana a station ba, idan kin fasa taɓa ni, dalla sake ni." ta fizge hannun ta sannan ta kalli Maa ta ce. "Karr ku za ci kallon ku kawai na ke yi, nasan komai har da zuwa gurin bokan da za kuyi infact har ta M.d kin mai, na sa ni, kallon ku kawai na ke." daga haka ta haye sama ɗauke da flask din Breakfast ɗin ta, wanda yau ma sun sha za ta yi musu ne, har ta Dad haka ya fita dan shi sauri ya ke yi ne. "Ki kira Zulai ta dawo bakin aikin ta." faɗin Maa tana zama, maganar Fancy ta daki kan ta. " Maa ki ba ni umarni da na ci uban ta." " Mu ci dai Hafsat, ni wallahi so na ke mu gana mata azaba." "Ku yara ne, idan ba ka iya kama ɓarawo ba to shi ya ka ma ka, mu bi komai a hankali, yanzu ko Tea ne musha sai muje gurin Malam daga can muje Malali." basu suka fita ba sai 10:12am, direct giɗan Malam Bulala suka je, ba su jima ba ya sallame su, bayan ya basu magunguna guda uku, na farko wani ruwa ne wanda zata haɗa da turaren ta sai ta shafa, kar ta yi ma kowa magana sai shi wanda aka yi aikin a kansa, na biyu kuma da zaran sun fara magana sai ta kai mai abun sha sannan ta sanya wannan garin a cikin, na uku kwalli ne wanda Halima ce za ta sanya sannan ta tabbatar haɗa ido da wanda take so, take komai zai yi dai dai.. **************** **************** Bayan driver ya kai su asibiti direct ɗauko Beasty, Beauty da Kandy ya yi sannan suka nufa gidan Fancy, a mota suke hira kwanin sha'awa. Karis ce ta ce " Sisters, Aunty Ramlat akwai mutum ci, kun ga yadda muke kwasan ilimi a wajenta kuwa." " Ma sha Allah sai ku da ge, kun ga mu da muka raina ta sai Allah ya nuna mana ishara da auran talakawa." faɗin Beauty sai Baby ta ce. " In sha Allah." Ta window ta kalli motan da ke bin su, Bugatti ce white wanda take hange Husty ke driving sai Hasty gefan ta tana latsa waya, a ta baya kuwa Butter ke kwance ta na barci. Ko da suka isa babban get ɗin Air Force Base, suka tadda Fancy tsaye jikin wata babban mota wanda har yau ba ta san mai shi ba wai yana UK, ita dai ɗakin Maa ta shiga ta ɗauko key shine ta fito, bayan an gama bincike motocin suka shiga cikin babban unguwan. bayan sun yi parking a babban gidan suka shiga ciki. Su tara ne dukkan su sun sanya Black Abaya dan haɗa baki suka yi. sunyi kyau dukkan su, duk da irin muhallin da wasu ke rayuwa amma babu ƙarya jiki yana cin mai daɗi, lafiyayyen girki Fancy tayi musu suka ci suna ta santi, "Wai Fancy ke ki kai wannan girkin kuwa?." Butter ta tambayi Fatima sai ta yi murmushi ta ce. " Ai yanzu na za ma expect." "Mu ma yanzu mun dage da girki sosai." Cewan Kandy, hira suka sha sosai suna mai taya Fancy da addu'a akan Maa. " Result ya fito, yau da safe muka duba." Dukkan su hankalin su ya koma kan Karis wacce suke jira suji score din su. " Ni 187, Butter 180 sai Baby 210." Murna ne ya cika su ganin sun samu score mai kyau balle Baby. END. [7/11, 17:40] 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊..............: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 54. BAYAN KWANA SATI BIYU ************* ************ Federal High Coat Office no.13, zaune suke su biyu suna shan soyayya, sai Hafsat ta ce: "Barrister in dai a shirye ka ke to zuwa Friday ba sai a ɗaura ba." ta kai nan ta na mai fatan jin abu me daɗi daga bakin sa, amma sai dai aka sin hakan ta ji ya furta. "Bar Hafsat ni kai na hankali na a tashe ya ke saboda ban aure ki ba, wallahi ji na ke kaman idan ban aure ki ba zan iya mutuwa." " To mai zai hana auran na mu?." Ta yi tambayan ta na kallon cikin kwayan idonn sa, sai daya sauke a jiyen zuciya sannan ya cire glass ɗin idon sa ya ce. "Hajiya, ta hana ni maganar aure, ta ce ban isa na yi ma matata kishiya yanzu ba......" " Wannan wani zancen banza ne." bakin ta ya furta hakan sannan ta miƙe tsaye daga sopa, gyalan ta ta ɗauka ta fita, office ɗin ta ke gefan wannan ta shiga, zama ta yi, jikinta a ma ce, tin washe garin da ta yi yadda Malam din su ya ce, ta yi yadda ya ce aikam washe gari suka fara soyayya da shi, sai dai ta na son su yi aure da gaggawa. Ringing wayanta ta fara yi, ta kalli screen din ganin 'MY MAN' ta ja tsaki sannan ta ɗauka, muryan sa mai taushi da natsuwa da ke kashe zuciyanta ya ce " Idan ki ka yi fushi da ni ya zanyi? ba zan iya rayuwa babu ke ba Hafsat, dan Allah karki gujeni ina ƙaun...." " Idan kana so na, to ka aure ni nan da kwanaki biyar....." Shi ma ya katse ta da ce wa " Hajiya ba za ta bari ba..." " Ka saki matar mana." ta na faɗin haka ta katse kiran sannan ta saki shu'umin murmushi, tattara kayanta ta yi ta wuce gida. A hankali ya leƙa tagar office ɗin, motanta ya hanga ta fita a coat ɗin, miƙewa ya yi jiki ba bu ƙwari sai ya tsaya ya na mai ciro wayan sa, number da aka sanya 'Hasty' ya ƙira, bugu uku ta ɗauka ta na kai kunninta, sallama ta yi ya amsa sai ya ce. " Hajiya Hassana mata ga yaya na Hassan, daga ke ba bu ƙari a cikin zuciyar sa." dariya ta sa ki ta na ce wa. " Wannan duk tatsuniya ce, ya aikin?." " Komai nomal yanzu ta wuce." " Hmmmm da ni ta ke wasan, sai ka han zarta nan da 35mnt zai farka kuma zai buƙaci wayar sa." " Nan da 20mnt In sha Allah za ki gan ni." da ga ha ka ya kashe kiran ya na tattara komai na yayan shi wanda yau a nan ya zauna dan wasa da hankalin Hafsat. (Toh fa???) ****************** ***************** _______*Zaune suke a cikin parlour jikinsu duk ya mutu, sakamakon abin da suka kalla yanzu, wato manyan-manyan asibitoci goma sha biyar daga jihohi daban-daban. A daren jiya aka konasu, abin mamaki shine ko rai daya ba rasa ba, sannan a gaba daya in da aka kona an ijiye babban banner wanda ke dauke da sunan RASH.* "*Innalillahi wa'inna ilayhi raji'un, wai wannan wani irin mugun mutum ne." fadin Hajiya sai Momcy ta ce. "*Allah ya isar ma masu hakkin su, kinga har da Asibitin da Meerah ta haihu.*" Jimami suka din ga yi, Meerah dake kwance a sopa, ta mike cikin sauri-sauri ta shige part ɗin ta, hannun ta wanda ya sha lalle suna dan sunyi babban shagalai wanda yarinya ta ci suna Surayya, amma suna ce mata small Ammee sabo da sunan mariganya Maman su Babba yayye ne. Wayanta ta dauka ta na latso number Zaki, wanda jiya ya dawo daga Abuja. "Umar ka ga abin da ke faruwa kuwa? " ta faɗa bayan ya ɗaga kiran. " Eh yanzu na ke shirin fita sai Sakeenat ta ke nuna min a waya." " Dan Allah kuyita tatara hujjoji akan komai, ina ji a jiki na akwai wani abu a ƙasa ayi bincike akan asibitocin." " Shike nan zuwa dare zan leƙo da hujjojin." daga haka suka yi sallama. ____________ Zaki kuwa kallon Sakeenat ya yi wacce ke jiran ta ji mai zai ce, " A tattara hujjoji sannan ya ba tun saƙon da ki ka tura." " Okh, ya je amma no reply." ta faɗa ta na ɗaure mai igiyan kalminsa. " Ka san kuwa asibitin da aka haifa a small Ammee har da shi." " Menene sunan shi.?" " SALMA CONSULTANT CLINIC." ya jin jina kai sannan ya ta rakasa har ya shiga sabuwar motarsa, sai ta koma ɗaki, kwanciya ta yi ta ɗan yi barci kafin nan brain ɗin ta ya yi refresh sai ta hau kan na'ura. END 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 55. *************** *************** "Kai ne ka aikata wannan aikin?." Ramlat ta yi tambayan ta na kallon Shuraim da ke kan kekensa, a hankali ya kalli fuskanta da babu wasa ta haɗe kaman ba ta san menene walwala ba, ya ce. "Ohhh Kifayaty kin san Ban san tambaya koh." " Na sani amma mai suka yi?." " Sirri ne." da ga haka ya shiga part ɗin sa akan keken, shiru ta yi ta rasa mai ya ka mata ta yi, ganin ya fito cikin sauya kayan jikin sa sannan ya nufa ƙofan da zai sa da shi da main parlour, kafin ya sa hannu ya murɗa handle ya ji ta ce. "Babban yaya." hakan yasa ya juya direction ɗin sa ya kalle ta, ita kam ta ci gaba da ce wa. "Dan Allah, Rash ya bar gangan jikin ka, aikin da ka ke yi mai kyau ne, amma babu wanda ya sa ni, dan Allah ka kiyaye ba zan iya rayuwa babu kai ba, kar ka cutar min da kan ka dan Allah." Duk da nauyin cikin ta amma a haka ta tashi ta shiga bedroom ɗin ta cikin gudu-gudu murmushi ya sa ki mai tarin ma'anoni, shi ko mutuwa zai yi sai dai ya mutu amma ba zak bar wannan aikin ba, zai ma iya ciwa salon ne zai sauya zai bayyana ma kowa amma babu wanda zai iya kashe shi, amma zai rage ka sa da. ______________ Karis na ganin Baban yaya ta miƙe ɗan guduwa ɗakin su amma taku biyar ta yi ta ji wannan muryan ta sa na. " Kiramin sauran kuzo." sai da ta haɗiye miyau sannan ya juyo ta gaishe shi amma bai amsa ba sai ta kuma ce wa "To Baban yaya." Room ɗin ta shige, shi kuma ya tsaya a gefan kujeran da Aunty ke zaune, gaishe ta ya yi ta amsa cikin sakin fuska, sai ga Hajiya ta fito da ga part ɗin Haidar dauke da baby, amsan ta ya yi yana gaida Hajiya ta amsa sai ta shiga kitchen, da yake kowa kwarji Shuraim ke ma sa babu mai wani zaman hira da shi ko wasa da dariya, shi ɗan serious at all the time, bayan sun fito su ka zauna kallon baby ya yi wacce ke kama da ƙaninsa kuma kama da ɗan sun biyo Pazar Q ne. "Ina kwana Yaya Shuraim." su kai gaida shi, da idanu ya bi ƙannan sa ukun wanda ya jima bai gan su ba sai yau. " Bilƙis je ki parlour na, jikin TV stand za ki ga wani leda ki ɗauko min." ta amsa ta na nufan in da ya aiketa, ba ta dau lokaci ba ta fito ɗauke da wani leda aje mai ta yi ga ban sa sannan ta koma in da ƴan uwanta ke zaune, wayan Aunty ne ya shiga ruri dan haka ta ɗauka ta na ba su guri, "Na ga result ɗin ku sannan jiya waec result ya fito." gaba ɗaya addu'a suke yi a cikin ransu. " Allah yaso ku , kuma kun so kan ku, gaba ɗayan ku kunyi kokari sosai, Allah ya ƙara basira." cikin farin cikin da ya wanke fuskokin su, suka amsa da 'Ameen'. "Karima kin ba Fadila 2 month dan haka zo ki sanya hannu a ledan ki ɗauki abu ɗaya a ciki." Da dan sauri ta matso ta sanya hannu tare da ciro wani abu da aka yi raping, sannan ya umarci Fadila da ta ɗauka sai Bilƙis, kowa kallon abin yake wanda yake kaman gift harda flower, Bilƙis na ta pick ne, Fadila Sky blue sai na Karima orange. " Kowa ta buɗe na ga." ai kan ya gama maganan sun fara warware raping ɗin, Karima da ta riga su han zari idanuwanta ta zaro, suma haka dan sun kammala buɗewa, waya ce dukka iri ɗaya Galaxy A05, amma ko wacce da kalan jacket ɗin ta, sai Sim pack wand duk ya sanya sim ɗin, sai kuɗi rafan dubu-dubu, sun ma rasa mai za su ce da sauri duk suka ajiye suka nufesa rungumesa suka yi suna mai godiya. "Ku karya jaririyan kunji." ya furta ya na murmushi, a ransa ya guɗira sauya rayuwar sa na gida, ya na so ya dawo kaman Haidar. " Mun gode, Mun...." " Kun san ban san godiya koh, In sha Allah da ga yanzu za ku ji daɗin rayuwa da ni, tin da kun dawo yadda na ke maradi, zuwa nan da 3 month za ku fara zuwa makaranta amma ba'an nan ba a Saudiyya za ku ƙarasa karatun, burin ku karatun nursing amma kun san me na ke so ku cimma?." da sauri suka amsa da "a'a" gabansa suka zauna suna mai jiran su ji abin da zai furta, sai da ya gyara kwanciyar Small Ammee sannan ya ce. "Ina da burin na ga kun za ma malamai akan addini, so nake ku karanci Islamic, kun yi hadda kun yi already da wasu littattafan, so na ke a kaiku can kuƙara bun ƙasa karatun na ku." " Babban yaya na amince dan ni ma zan yi alfahari da za ma na Malaman addini." faɗin Baby sai Karis ta ce " Ni ma na aminci In sha Allah za mu dage." sai suka kalli Fadila wacce bata yi magana ba, " Idan bakya so babu dole zan iya kaiki U.S dan ki yi na ki karatun likitancin." Babban yaya ya furta sai Fadila ta ce "A'a Babban yaya, ina so, ji na ke kaman mafarki na ke, wai da kai muke hira akan rayuwan mu." sai kuka ya kwace ma ta, sai da ya sauke a jiyan zuciya sannan ya ce. "Na sallame ku, and ku shirya gobe za'a kaiku hutu wani gida, wata 1 za ku yi sai ku harhaɗa kayan ku." suka amsa sannan suka shige Room ɗin su, murna duk ya cika su, sun rasa ina zasu sanya ransu dan murna, har sun cire hijabs ɗin jikinsu suka mai da sannan suka fita kowa ni part sai da suka je suka nuna musu, Hajiya, Mom, Momcy, Aunty, Meerah, Ramlat sannan suka je gidan Zaki ita ma Sakeenat suka nu na mata. ***************** ************* _________ "Gaskiya Babban yaya yana ji da ƙannan sa fa." faɗin Sakeenat wacce ke kan kujera ta tsaya da duba saƙon da ya shigo ta na kallon wayoyin na su, " Bamu number ki Aunty SK." Karanto musu ta yi suka yi saving sannan suka koma gida san su ba ta guri ganin aiki take yi, Idanu ta zaro ganin saƙon da ta tura ma 'Rash' an yi reply da 'mun gode amma ku sa ni Rash baya neman taimako gun kowa sai Allah, kuma nan da kwana biyu zai bayya ma kowa.' abin da ta gani kenan, ai babu shiri ta janyo wayarta ta kira number Zaki, bayan ya amsa ta sanar mai da reply din sannan ta ce "Akan asibito cin kuwa ko sanne da mugun aikin da ake yi a ciki, a zahiri babu wani hujja amma a baɗini akwai abubuwa da yawa, SALMA CONSULTANT CLINIC ne kawai na gano na su, akwai wasu magunguna da suke amfani da su wanda babu sa hannun Nafdac a ciki, kuma ana zargin shugaban asibitin da safaran jarirai." "Ya-salam zan kira zuwa anjima." Kashe wayan ta yi, tana godiya ga Allah ya turo mu su Rash. End 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [7/13, 06:32] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 56. **************** **************** Malali ____________ Motar Hafsat ce ta yi parking a bakin get ɗin gidan su Salma, ba su san me ke faruwa ba amma sun san babu lafiya, ciki suka shiga bayan sun gaida mutane maza da mata a cikin gidan kaman ana wani taro, sai dai taron kowa ya gani yasan ba na lafiya ba ne saboda fuskokin jama'ar gurin babu annuri. Ganin mutane da yawa a part ɗin Maman Salma sai Hafsat da Halima suka shiga na Salma, Salma ce kaɗai kwance kan babban bed ɗinta, hawaye na sauka a fuskanta, ganin su Halima ya sa ta tashi ta zauna, Halima ta matsa gaban ta tare da ce wa. "Salma me ke faruwa ne a gidan nan?." wani sabon kukan ne ya kwace mata, sai da suka rarrasheta sannan ta faɗa musu. " Baba na ya rasu sanadiyyar accident zuwa Abuja, ɗazu aka kawo gawarsa." "Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un." Hafsat da Halima suka furta a natse sai ta kuma ce wa "Kafin a faɗa mana rasuwar mun wayi gari da Asibitin Momy na ya ƙono ƙur mus." Salati suka dinga yi suna jin tausayin Salma dan mahaifi babban bango ne na rayuwar ɗa, haka jigo ne mai ƙarfi, su ma sun ɗanɗana wannan raɗaɗi. ________ A part ɗin Doctor kuwa ta suma yafi sau biyar, da ƙyar ta samu hankalin ta ya kwanta, ta rasa ina za ta sanya kanka, komai baya ma ta daɗi, a ce abu biyu a lokaci ɗaya, duk da dukiyan da ke asibitin bai da me ta ba kaman mutuwan Askira. _______Dady da wasu manyan-manyan mutane ne cike da babban haraban gidan dan ba su jima da dawo wa kai sa makwanci, hatta His Excellent Aliyu Haidar Abdulqadir sun halacci wannan jana'izan, Dady wanda ya ke ganin abin kaman a mafarki, dan jiya sun yi sallama amma sai gawan sa aka kira yaje ya ɗauko, mutuwa ta farar ɗaya ya yi, babban mota ce ta bi ta kan tasu motan, ta ke Askira da driver su ka mutu bayan sun yi fata-fata dan ko kallo ɗaya ka musu ba za ka ƙara ba, babu abin da yafi tsorata Dady fa ce sanadiyyar tafiyar Askira, sun yi plane ne da yaje Abuja gurin wani babban boka, gashin kan His Excellent Aliyu suka ɗauka za suka kai ayi tsafi da shi.. (Allah ya kyau ta, ya kare mu da mugun ɗabi'a da mutuwa akan hanyar da bai da ce ba---- Ameen ya Allah.) ******************** **************** ABUJA _________ Cikin gaggawan ta gama shiryawa, a parlour ta gansa, kallan shi ta yi ta ce. " Dear na gama." bai ce komai ba ya ɗauki trolley ya yi waje, bayan sa da ta bi da ido ta ƙare mai kallo, bayan sa tabi ta shiga mota take motan ta hau tafiya. " I'm sorry da ɓata maka rai, ɗan......" " It's ok, yanzu direct Kaduna za mu je, kin ga ke kinyi barci, nima ki bari na yi yanzu." "Okh." ta furta ta na sakin murmushi dan ta na jin wani sanyi a ranta, ba ta san mai ya sa ba amma har ga Allah ta na jin wani irin abu haka a cikin jikinta tin da suka shigo Nigeria a jiya. **************** **************** KK GRA _________ 9:23pm, babu wanda ya tan kasa, kira na 8 kenan amma ba ta shiga number, Hasty ce ta ƙalla Husty sai ta yi ma ta alama da ido, take ta miƙe ta shiga part ɗin ta, kunna wayarta tayi tana zama kan sopa, take wayar ta hau ringing sai da ta saki shu'umin murmushi sannan ta ɗauka. " Alhamdulillah." Yusuf ya faɗa da ƙarfi dan jin babynsa ta ɗau kiran, zama ya yi gefan Hajiya ya na ce wa, "Hajiya ta ɗauka ta ɗauka, Assalamu alaikum." Hasty da abu biyu ya haɗe mata dariya da kishi, ta na dariyan tarkon da suka yi mai sannan kishin kuma ta na tinanin ashe haka ya ke ma waccan ƴar iskan wato Barrister Hafsat. " Yusuf." yaji ta furta, duk da number ta ce sai da ya kuma kallo sa bo da jin muryan kaman ba na ta ba. "Mai ya sa mi voice na ki.?" " Mura na ke yi." Hasty ta furta ta na gyara kwanciyar ta akan sopa tare da rage murya. " Okh, ya kike ya yau?." Ya furta har jikin sa ya na rawa. " Am fine what of you?." " Steady, yanzu kin ganni kusa da Hajiya, dan Allah ki gaidata kin ji, kuma ki roƙe ta na aure ki kin...." " Wait Yusuf, kasan mene ne?." " A'a Queen, in ba za ki iya gaida ta ba babu damuwa kinji." ya furta da dukkanin gaskiyar sa, ba Hasty ba haryta Hajiya, Husty da Yunus sunji mamakin abin da ya faɗa. "Ni zan ce ma wannan matar dalla gyaleni da maganar ka ba dai ka na so na ba." " Sosai ma, wallahi i love you." "Ina son gobe da kai da matar ka kuje Saudiyya, so nake ko izu 30 ka haddace a kan ka sai mu yi aure." "Hadda kuma, ai na hadda ce Alqur'ani." Husty ta dai-dai kan ta sannan ta kuma magana. " Eh na sani so nake ka dawo farko, kuma da wa su takaddun, zuwa lokacin sai muyi aure abin mu." " Hakan ya miki." " Sosai ma." " An gama gobe zan tafi." " So nake in kaje karka ƙirani har sai randa ka dawo, so na ke ka dawo Shaikh." "Hajiya kin jifa, na faɗa miki ustaziya ce." ya kai nan ya na mai da wayan kunne, Hajiya dai dai ganin ikon Allah suke. " Ka tafi da Hajiya maybe before ku dawo ta so ni." " Insha Allah, sai dai ba zan iya tafiya gobe ba in ban gan ki ba." ta ke zuciyar Hasty ta buƙa sai dai jin abin da Husty ta ce ya yi ma ta daɗi dan wayan a speaker ya sanya "Aure na ko gani na wanne kafi so?." "Auran ki." " Fine, good bye." daga ha ka ta katse kiran, jingina kansa ya yi jikin kujera ya na dafa kan na shi sai ya ce " Hajiya ina son Hafsat, bazan iya saɓa ma umarnin ta ba, gobe zamu je saudiyya, zanyi ma wani abokina waya yanzu da ya shirya min komai." Babu wanda ya tan kasa har ya gama, sannan ya miƙe ya shiga part ɗin su, da Idanu suke kallon juna, Hajiya har ranta ta kejin babu yadda za ta yadda ya aura yarinyar da ya ke so, ti na abin da Malam Zakari mai maganin Hausa da yazo ɗa zu ya ce musu "Sihiri ne ya ke wayo a gangan jikin sa, idan kuna neman lafiyansa to abu uku za kuyi Insha Allah komai zai yi dai-dai, na farko, a yi ne sa da shi, yadda karma su haɗu da wacce ta yi sihrin, na biyu ya yawaita karatun Alqur'ani da wasu Addu'oin, na ƙarshe shine ruwan zam-zam, kullum a dinga mai addu'a a ciki sai ya sha, babban matsalan ba musan da mene ne aka yi sihirin ba amma insha Allah in ku kayi yadda na ce za'a dace..' " Hajiya gobe sai ta fiya, dama na gama shirya kayan ki, idan da akwai wasu abu da kike so sai ki faɗa." Hasty ta faɗa cikin sanyin hali sai Hajiya ta ce. " Ban san na ga kin shiga damuwa, zo." tayi mata alama da hannu, miƙewa ta yi ta nufa sai ta rungume ta, take kuka ya kwace ma ta, Hajiya ba ta rarrashe ta har ta gaji da kukan dan kanta, sai da ta yi yadda ta ke so tukun ta yi shuru, Husty ta yi tsaye da ga gyefan Hajiya tana sauran kukan Hasty wanda ya ke karya mata zuciya sannan ta ce. " Hasty ki yi haƙuri, daɗin abin munyi maganin komai cikin sauƙi." ta kai nan tana murmushi dan ti na ɗazu da suka sanya number ta a wanyan Yusuf sannan suka yi saving kaman yadda ya yi na Barrister Hafsat, sai sukai deleting bayan sun yi blocking ɗin ta. " Yanzu Sim ɗin sa kawai ya rage na cire na ba Husain, bara na duba shi." da ga haka ta miƙa ta shiga part ɗin su, sauke a jiyan zuciya Hajiya ta yi tana mai ce wa. " Koma wace ce Hafsat ɗin nan, ba yarin yar aure ba ce sam." " Gaskiya kam, abin haushin ba ta biyo hanya mai kyau ba....." " Wallahi Husaina ba yadda ma zan bari Yusuf ya yi ma Hassana kishiya yanzu, ba ta yadda zan yadda." " Allah ya sa mu dace, yanzu Hajiya mu kaɗai za ku bari?." Faɗin Husty sai Hajiya ta ce. " Eh mana, ko dan wan can ƴar iskan dole ku tsaya dan Yunus ya koya mata darasi." End 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 [7/13, 12:13] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 57. ********************** ******************* Malali " Hafsat ki ba ni key ɗin motar ki, ku bi Dady zuwa gida ni anan zan kwana." Maa ta faɗa cikin sanyin jiki sai Halima ta ce. " Ni ma anan zan kwana saboda na ɗauke ma Salma kewa, Hafsat ta tafi kawai." " A'a gobe ma wuce duk kan kawai." Hafsat ta faɗa ta na gyara zaman ta, sai Maa ta kuma ce wa. " Shike nan ba ra na ce ya tafi, ku fito kuci abinci toh." da kai Halima ta ɗaga, sai Maa ta fita, Salma da ta fito wanka ɗaure da towel sai mayafi ta ce. " Gaskiya na ji daɗi, ni har gobe ba zan bari Halima ki ta fi ba." " To mai zan miki anan ɗin.?" " Kawai dai, kin san kaf familyn mu banda ƙawa, gidan nan gaba ɗaya babu age mate ɗin na kinga." " Gaskiya ko sati ɗaya ta miki, gobe sai ta yi ma Maa magana." Hafsah ta furta ta na kuma mai kira na biyar amma duk abu ɗaya ya ke ce wa, an yi blocking ɗin ta. ****************** ******************* Air Force Base ___________ Da ikon Allah ya isa gida, dan har yanzu mutuwan bai wani sa ke sa ba, parlour ya shiga bayan ya fito daga motan, babu kowa kamar yadda ya yi tsammani, Room ɗin sa ya shiga bayan ya yi wanka ya fito dan samun abin da zai ci, a kitchen ya samu Fancy sai ya ce ta kawo mai abinci, takaici ya sa ta kasa magana sai Indomie ta samu ta yi mai ta kai mai parlour. " Dady Ina su Halima?." Fancy ta tambaya ta na jiran ya ce ga in da suke ta bi bayan su. " Suna gidan rasuwa, sai gobe zasu da wo." " Waye ya rasu?." M.d ya furta bayan ya gama sauka da ga stairs. " Askira." kusan suman tsaye M.d ya yi ya na mai ƙara furta sunan 'Askira', Dad ya ɗago idanunsa ya yaƙara tabbatar mai da 'eh', salati M.d ya shiga yi a fili, Dad ya bashi labarin komai, mutuwar ta bigesa sosai hatta Fatima wacce ba ta san waye ba amma ta ji mutuwar. " Allah ya jiƙan sa, na za ci sun dawo ne dan na kammala girki, na shiga yanzu na ga babu duk ka flask ɗin." " Babu! to wa ya ɗauka, ko dai kin manta ne?." M.d ya yi maganan ya na kallon Fancy sai ta ce. " Haba da hannuna na zuba amma kafin na dawo na ga babu, na za ci sune ai, ka duba......" " Wait.. kodai an shigo gidan ne?." " Dad sai a rasa mai za'a ɗauka sai Abinci, kawai ki sake du bawa dai." ta kaici ya sa Fancy ta yi shuru sai suka ji magana kaman daga sama, cikin zazzaƙan muryar sa da lafazi " I'm sorry ban san na ki ba ne, ni na ɗauka." gaba ɗayan su kallon sa suke yi cikin mamakin yaushe ya shigo gidan, a hankali ya sauka ya na gyara agogon hannun sa. " A.A yaushe ka dawo?." . " Dama surprise zan muku, ɗazu na shigo, bro na ga kayi ƙiba ne." Murmushi M.d ya yi ya ce. " Gaskiya da ka faɗa mana mu tarbeka sosai, kai ne ai kayi ƙi ba sosai." " Ina wuhi Dad." Ba Dad ka ɗai ba harta M.d sai da ya ware idanu, wai A.A ne ke gaishe da Dad yau. "Me naji ka ce A.A?." Dad da yake jin kaman ƙunnuwan sa sun yi mai ƙarya ya tambaya sai A.A ya riƙon hannun Dad ya ce. " A.A ɗin da, daban da ne da na yanzu, Dad na sauya fiye da tinanin ku, na dawo yadda zaku yi alfahari da ni." Dad rungume Auta ya yi ya na zubar da kwalla mai tarin ma'anoni masu yawa, A.A wai shine ya ke mai magani cikin taushi da na daman abubuwan da yake mai, M.d ma hawaye ya share ya na jin dama Maa suna nan ya san sai tafi kowa farin ciki. a hankali ya raba jikinsa da na Dad ya sa hannun sa ya share hawayen da ke zu daga idanun Dad. " Ban san kana zubar da kwalla kaji." sai ya kalli Fancy wacce ke kallon sa, murmushi ya sakar mata ya kuma ce wa. "Amaryar mu ce?." " Ina wuni." Fancy ta furta duk da tana jin haushin kwashe mata flask da ya yi ɗan lafiyayyen girki ta yi. " Ai in na amsa na yi rashin kunya kina matar yayana ai ni zan gaishe ki, ina wuni." A.A ya yi maganar ya na miƙewa sannan ya ta ka zuwa gaban ta. "Alhamdulillah." ta furta da gyar dan A.A irin mutane ne masu yi ma mutum kwarji a kallo ɗaya. "Gaskiya Yaya ka iya zaɓe, she looks innocent, beautiful, wow me sunan aunty ta wa?." Ya kalli M.d ya mai murmushi, M.d da yake ganin abin da A.A yame yi kaman a mafarki ya ce. "Fatima." " Wow Fatimatul zahra'u, suna mai matuƙar daraja, sunan ɗiyar manzon Allah." Suka amsa da 'saw' " Ban ga su Maa da su Hafsat ba." " Suna gidan su Salma, mahaifinta Allah ya yi mai rasuwa." Dad ya furta annurin fuskansa na ɗauke wa, take shima AA annurinsa ya rage. " Subunahllah, Allah sarki Allah yajikan sa." " Ameen ya Allah." ********************* ******************** _____________ Tun safiyar yau suka kammala komai misalin 10:12am mota ta ɗauke su, su dai nasu ido kawai dan wani saɓon unguwa sukaga an kaisu, ko bayan sun shiga babban gidan wanda sukai ta kallon coumound ɗin gidan mai kyau sosai, bayan sunyi parking Baby ce ta fara fitowa sannan suma su Karis, fuskokin su ɗauke mamakin nan ina ne. " Sani nan ina ne wai?." Butter ta yi maganan ta na kallon driver, sai ya ce. " Oga ne ya ce na kawo ku na wuce, ni kai na ban sani ba gaskiya." fitowa ya yi ya firfito musu da kayan su, ba yadda suka iya babban ginin da ke tsakiyan haraban wargajejen gidan suke kallo, door bell Karis ta danna, sai su kaji an amsa, suna tsaye har aka aka buɗe, wata ƴar yarinya su ka gani sa'ar su tsaye tana gaida su, ta ce su shigo dan ta san da zuwan su, jikin su a mace suka shiga dan ita yarin yar ko ganinta ba su taɓa yi ba, ma sha Allah parlour ne wanda yake ɗauke da three seaters na kujeru, amma duk da haka akwai space a parlour, a haka suka zazzauna a kujerun, sai wannan yarin yar ta shiga musu da kayan su wani ɗaki. " Ko dai munyi ma Babban yaya laifi ne shine ya kawo mu nan dan ya hora mu?." Karis ta faɗa idon ta cike da kwalla, sai Baby ta ce. " A'a in sha Allah ba ha ka bane sister." Kafin Butter ta ce wani abu sai wannan yarin ta dawo parlour ta na murmushi sannan ta zauna daga gefan su ta ce. " Yanzu zasu dawo, kafin nan mai za ku ci?." " A'a Alhamdulillah a ƙoshe muke." ce wan Butter, babban TV da ke aiki ne aka sanya wani shiri mai daɗi, dan haka suka mai da hankali gurin kallon wani Nigeria Film me suna Treasure in the sky. END. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 58. ___________ "Honey, sai ka sauke ni a nan." Ba tare da ya ce komai ba, ya yi parking sannan ya ɗago idanunsa yana kallonta. Hannunsa ya kai kan nata, tare da ja da rigarta, yana cewa: "Don Allah ki yafe abin da su Maa suka miki. Suna gidan mutuwa amma babu Allah a ransu." "Honey, kar ka damu, ya wuce, wannan Black car ɗin Babban Yaya ya ce na hau." "To, don Allah ki kula da kanki. Idan za ki dawo, ki kira ni please, sai na zo na ɗauke ki." "In sha Allah, Honey. I love you." "I love you too." Ya sunbaci hannunta, sannan ta sauka. Ta ɗan yi tafiya kaɗan sannan ta shiga ɗayan motar. Sai bayan da ya ga motar ta hau titi sannan ya ɗauki nasa hanya. Tunani iri-iri ke yawo a ransa—har na abin da Maa suka yi wa Fancy. A gaban mutane suka tozarta ta da cin mutumci. Bai taɓa ganin ta zubda kwalla ba sai yau. Hijabi fari ne ta sa, suka zo ba mata manja. A hanya ya tsaya ya siya mata wani. Addu'o'in da yake yawan yi ne yasa yanzu baya jin daɗin halin su Maa balle yadda suke wa Fatima. *************** *************** "Ashe za ki iya tafiya ki bar ni, Hasty?" Sai ta fashe da kuka tana rungume Hassana. "Yanayi ne, amma da bazan iya ba, da zarar komai ya wuce zan dawo." Sannan ta saki ta, ta ja baya. Tun da suke tare suke rayuwa – dai dai da kwana gu ɗaya suke yi, sannan ba sa iya yi ba tare da juna ba. Idan ɗaya na rashin lafiya, tare ake kwantar da su. Allah ya ga ba za su iya rayuwa babu juna ba, shi yasa har ya ba su ƴan biyu kuma gida ɗaya. "Menene abin kuka? Kun ga yanzu sai ku sha amarci ke da Husain." "Amarci kuma, Hajiya?." Sai sabon hawaye ya zubo, Husain ne ya riƙo ta ya saka ta cikin mota sannan suka bar gurin. Shi ma zuciyarsa a karye take, ɗan uwan sa guda, wata mace ta sauya masa rayuwa. Hannunsa da ke dungule ya buɗe, ya kalli SIM card ɗin Hassan. A ransa ya ce, "Dole na koya miki darasi, Hafsat kin taɓo ni wallahi." Har bakin get ɗin ya kaita. A lokacin har ta bar kukan. Dai dai nan Fancy ita ma ta sauko daga motar da ke gabansu. "Zuwa yamma zan dawo. Babban Yaya zai sa a kawo ni gida." "To shike nan. High Court za ni yanzu, akwai abin da zan yi a can." Sai ta ɗaga masa kai, Hawaye ya kuma gangarowa daga idonta, sai ya share ta yana cewa: "Na ce ban so. Idan kuma za ki zubar min ne, to ki tara min wallahi. Ban yadda a zubar min da su a banza ba." Murmushi ta yi sannan ta fita daga motar. Ganin ta na zubar da hawaye, Fancy ta rungume ta tana cewa: "Menene sister? Waye ya taɓa min ke?" Ina! Sai sabon kuka. A hankali ta zame jikinta ta nufi motar Husain da ke kallon su. Kafin ta ƙaraso, ya janye gilashin window, ya san da ɗan haka. Ya yi mata murmushi yana cewa: "Fatima koh?, Kin san ban ga ne ku sosai." "Eh, me ka yi mata?" Ta furta, ranta a haɗe. Murmushi mai sanyi ya yi yana cewa, "Ni babu ruwana. Hasty ce." Take ta tuna da abin da suka tattauna ɗazu a group na tafiyar Hasty. Sai ta yi masa sallama ta koma wurin Husty. A tare suka shiga cikin gidan, shi kuma ya wuce. Suna jin doorbell dukansu suka mai da hankali kan ƙofa. Yarinya ce ta je ta buɗe, sannan suka shigo. Su Butter suka hau murna ganin ƴan uwansu, sai hankalinsu ya natsu. "Matar Barrister, me ya same ki?." In ji Karis—haka take ce mata. "Sai haƙuri, Hasty ta bar ƙasan nan," in ji Fancy. "Oh, toh. Allah ya tsare. Na manta ne ai," Butter ta furta. Take kuma aka buɗe ƙofa, mata uku suka shigo cikin ɗinkin atamfa iri ɗaya—Beauty, Kandy da Beasty. Suka hau ihu da murnan ganin ƴan uwansu kamar sun jima ba su haɗu ba. "Wait! Wait! Wait! Wai nan gidan ku ne?" Karis ta faɗa tana kallon su Beauty. Sai suka ɗaga mata kai. "Ai an ce kar mu faɗa muku ne. Babban Yaya ne ya siya mana wannan gidan sannan ya haɗa mu a guri ɗaya. Can na Beauty ne, wannan kuma na Kandy, sai wannan nawa." Beasty ta faɗa tana nuna ɓangarori uku. Sai ɗaya da ke gefe, anan aka kai kayan su. "Ma sha Allah. Allah ya saka da alheri, na muku murna, Sisters." "Thanks, Fancy. Hmmmm, Husaina, za ki iya saki jiki da mu koh? Yadda kuka san an raba ta da ruhinta." "Hassan ita ce numfashina, ji nake ba zan iya rayuwa babu ita ba." "I'm sorry. Mun san yadda kike ji, sis. Dan shaƙuwarku na da ban ne." Kandy ta kalli wata budurwa ta ce: "Zubee, fatan kin yi arranging komai?" Da kai ta amsa sannan ta shige ɗakin. "Ina kuka samu yarinya?" Fancy ta tambaya tana cire hijabin jikinta. "Kyauta aka ba mu ita—marainiya ce. Babban Yaya ya ba mu ita. Sunanta Zubaida. Ba ta da damuwa. Komai ka saka ta, za ta maka, g son aiki da biyayya." "Ma sha Allah." Daga nan suka shiga duba ko ina na gidan. Irin dukiyar da aka narka ba a magana. Gida ya haɗu har ya gaji da yaɗuwa. Bayan sun gama duba ko ina, suka zauna suna hutawa. Bayan nan suka tafi dining area—wasu tsararrun abinci da abubuwan sha na musamman ne a zagaye gurin. "Ni yaushe za ku zo min hutu? Gashi nan da ɗan lokaci sai Saudiyya kenan," in ji Fancy. "Da Babban Yaya zai yadda, ko one-one week sai mu zo," Baby ta ce. "Mu kira shi to, mu ji," Karis ta ce tana ciro wayarta. Suka nuna mata lambarsa da aka ajiye da sunan Boss. Ta dannata, da mamaki sai ta ji yana ringing—abin da da wuya ka kira ka same shi. Bayan kiran ya katse, sai ya kira ta. D ta ɗauka, muryarsa ta daki kunnensu: "Ina ji." "Assalamu alaikum. Ina wuni. Da ma Fancy ce—oh sorry, Fatima ce. Ta ce tana so ko 2 days ne muje muyi mata kafin mu dawo." sai Karis ta yi shiru don jin me zai ce. Sai bayan kusan minti 2 sannan ya ce: " Ba Husaina wayan." Da sauri ta miƙa mata, dan tana kwance a gefe ta kuma ta ƙi sakin jiki. "Babban Yaya..." "Hassan ta faɗa min komai. Me yasa ba ku sanar da ni ba? Ku fa ƙannai na ne, wanda nani muku kallon yara ba, Ni nan jagoranku ne. Ko wani irin damuwa gare ku, ku faɗa min kun ji? Yanzu dai na so a shigo da ku da surprise ɗin ku, sai dai na lura bakya so ke." "A'a Babban Yaya, muna so." "Ok, kibar damuwa, ban so, yanzu za a kawo muku." "Mun god—" "Ban son a godiya you know. Allah ne abin godiya, In ma godiyan ne, Auntyn ku za ku nawa, Ita ce ta sauya ni." Kafin su ce komai, ya katse kiran. Shiru ya ratsa wurin. "Ni ban san me ya kamata mu yi ma Aunty Ramlat ba, dan mu saka mata," faɗi Kandy. "Muyi mata fatan ta sauka lafiya kawai. Daga nan sai mu shirya mai za mu yi." Misalin 6:10pm, bayan sun gama shirin tafiya, sai suka ji motoci na shigowa gidan. "Ɓaƙin yamma kuka yi ne?" Butter ta faɗa. "Ko dai su Ya Adam ne?" Karis ta ce, sai Kandy tace. "Anya? Let’s go and check."Daga nan suka fita zuwa compound. Da idanu suke kallon matasa hudu—kowanne ya fito daga sabuwar mota mai ƙyalli, dukkan ƙira Bugatti. "Assalamu alaikum." "Wassalamu alaikum. Boss ne ya aiko mu."Ɗaya daga cikinsu ya miƙa key ya ce: "Wannan na Madam Hauwa'u." Beauty ta amsa da mamaki. Sai na gefensa ya ce: "Wannan na Madam Husaina." Kandy ta amsa mata domin su ba su fito ba. Haka suka ba su, sannan suka wuce. Da gudu-gudu suka koma ɗaki suna cewa: "Mota! Mota Babban Yaya ya siya mana!" Gaba ɗaya suka fito—Beauty, Beasty, Kandy, Fancy da Husaina. Kowa ta shiga nata, suna dubawa a ciki kowa ta samu takardu, sannan suka duba. Fancy da Husaina su na makaranta (HND). An gama komai. Fancy Polytechnic wanda ke opposite da Air Force Base. Husaina kuma a Malali, kusa da gidan su. Beauty, Beasty da Kandy sun kammala karatu. Kandy Journalist ce a AIT TV. Beauty karatu ta yi a Fashion and Design, ta kaddun wani shago ne a wani plaza. Beasty kuma za ta haɗa aiki da karatu—likita ce ƙarama, za ta fara aiki a wani babban asibiti, daga nan kuma ta ƙara ilimi a fannin lafiyar mata. End. 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀɪᴏɴ (ᴊ.ᴡ.ᴀ)💪 ʀᴜʙᴜᴛᴜ ʙᴀɪᴡᴀ ᴄᴇ ᴅᴀɢᴀ ᴀʟʟᴀʜ, ᴊᴀᴊɪʀᴛᴀᴛᴛᴜ ɴᴇ ᴋᴀᴡᴀɪ ᴋᴀɴ ɪʏᴀ ᴀᴍғᴀɴɪ ᴅᴀ ᴡᴀɴɴᴀɴ ƙᴀꜱᴀɪᴛᴀᴄᴄɪʏᴀʀ ʙᴀɪᴡᴀ ꜱᴜ ꜱᴀᴜʏᴀ ᴛᴜɴᴀɴɪɴ ᴀʟ'ᴜᴍᴍᴀ ᴄɪᴋɪɴ ꜱᴀᴜƙɪ.✍️ 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ĎĂĞĂ ĂĹƙĂĹĂМĨМ РŔĔŤŤŶ ŚĶ ✿◡‿◡✿ [Sakina Abdullahi] ✿◡‿◡✿ typing.... Page 59. ************** *************** Driving back home, take yi a natsa har ta isa gida. Ta shiga part ɗinta kai tsaye, ta gabatar da sallah sannan ta dawo parlour. Ganin fes ko'ina an gyara, ta yi mamaki sosai. Ta leka kitchen, ko za ta ga mai aiki, amma babu kowa. Sai ta dawo parlour. Take aka buɗe ƙofa aka shigo – Halima, Hafsat da Maa ne. "Wato sai yanzu suka dawo," ta raya a ranta. Ta ɗauke kanta daga kansu, ta mai da hankali kan TV. "Baki iya gaisuwa ba ne?" Hafsat ta faɗa cikin isa. "Ban iya ba, Hafsat Ai na ga kin iya sallama." Fancy ta amsa a da ke. "Yarinya nan ba ta da mutumci fa." Halima ta furta tana cire gyalenta. Sannan ta kashe TV ɗin da ke aiki, ta yi magana da zafi zafi :"Ai kina da TV a part ɗinki, sai ki koma can. Masu gida sun dawo." Fancy da takaicin abin da suka mata ɗazu ya dawo ƙal a ranta, kawai ta tsinka ma Halima mari har sau biyu. Hafsat yake tayo kanta. Nan fa suka hau fada sosai. Maa dai tana kallon ikon Allah. Sun jibga juna babu laifi, balle Hafsat – har bakinta ya fashe. Fancy kuwa duk ta ta sha yaƙushi dan Hafsat akwai farce masu tsayi. Da yake window ɗin glass ne, ganin M.D ya a batanan gidan sai Fancy ta saki shu'umin murmushi. Kafin handle ɗin ƙofa ya yi ƙara, ta zube ƙasa tana kurma ihu: "Don Allah ki yafeni, Maa ki ɗauki za ta kashe ni. Wayyo Allah!" Ta na kuka da ihu. Su dai ido suka zuba mata. Sannan suka lura da wanda ya shigo – M.D ne. Nan suka fahimci in da zancen ya dosa. "Hafsat, kina hauka ne? Uban me ya sa ki dukan matata?" Ya furta cikin fushi, sannan ya ɗago Fancy daga ƙasan. Sai ya tsinka ma Hafsat mari ta ke ma ta buɗe baki tare da nufansa. "Uwarka ce ta sanya ta! Akan wannan kake maran ƙanwata Muhammad? Kana hauka ne? Za ka bugata akan wannan yar iskar? Wai da me take taƙama ne? Ita ɗin wata tsiya ce.". "Maa, babu ruwanki a ciki. Tunda kina kallo za ta kashe min mata kuma tana ɗauke da juna biyu, salan ta zubarmin." Maa ta buɗe baki tana maimaita:"Juna biyu?." cikin sauri Muhammad ya ɗaga mata kai ɗan ƙara tabbatar da hakan. "Wannan hayaniyan fa dan Allah, mutum shi ba zai huta ba wani lokaci in dai yana gidan nan."Suka ji saukar muryar A.A. Maa da su Halima suka yi mamakin ganin sa. "Auta, yaushe ka dawo?" Maa ta faɗa tana kallon shalelen ɗanta cike da so da ƙauna. Sai da ya iso gabanta sannan ya ce:"Maa, jiya na dawo. Na yi kewarki sosai." Ta riƙe hannunsa, suka zauna."Allah sarki. Ashe za ka dawo. ni kam har na cire rai, Yaya kake?" "Lafiya, Maa." "Shine ka kasa faɗa mana dawo wan ka? Uhmmm Sirikin ka Allah ya rasu." Ta kai nan maganar tana kallon Muhammad da fushi tare da dalla mai harara. "Maa, na sani ai, Sun faɗa min." "Shine ba ka zo ba?." "Ai na yi masa addu'a." "Ayya. To ai ko Doctor ka je, ka ma ta’aziyya. Sannan ka ga Salma. kar kaga yadda ta ko ma baiwar Allah duk ta sauya." "No, Maa. Ni fa ki daina haɗa ni da Salma. ba zan aure ta ba." Take ta saki hannunsa, annurinta ya ɗauke. "Ban gane ba. So kake ka ce ba za ka aure ta ba? Why?" "Because I have a wife. I'm a married man." Ba Maa kaɗai ba, har sauran na parlour jin zan cen suka yi daga sama. Hatta Dad da ke saukowa ya tsaya. "Me? Ban gane ba. Ka yi aure da iznin wa?" Maa ta tambaya da faɗa. "Eh, na yi aure, da iznin kaina." "Enough!" Maa ta faɗa da ƙarfi. A.A ya juya, ya nufi stairs da sauri. Sun yi zaton ba zai dawo ba, sai gashi ya dawo da hanzari, wata kyakkyawa yarinya na biye da shi. Fara ce ɗal, doguwa, tana da kyau sosai. Sanye take da doguwar riga ta material, tana kallo kamar baturiya, balarabiyya ko shuwa-arab. "Baturiya ka aura?." Hafsat ta tambaya, amma bai ce komai ba. Bayan sun gama sauka, A.A ya ce:"This is my Dad and my Mom, then my brother, his wife, and my sisters." Ya nuna mata su duka. Sai ta saki murmushi, ta gaishe su: "Good evening Dad, Good evening Mom and all together." "A.A kana hauka ne? Wa ya ɗaura maka aure da kafira?" "I'm Muslim. My name is Airah Abdullahi." Airah ta faɗa da mamakin yadda ba su san ta ba. "Innalillahi. Abdullah ka cuce ni? me zan faɗama Doctor da Salma? Next Friday mai zuwa zan aurar da ita ko kana so ko ba so, yadda zaka yi da wannan kai ka sani." "Hmmmm. Never! Ba zan auri wannan yarinyar ba, Kuma in baki sani ba, Maa, ki sani yanzu, Salma tana shaye-shaye. Salma tana bin maza. Salma na—" abin da ba ta taɗa yi masa ba shine yau ta mai, mari, Hannu ya ɗaura a gurin sannan ya ce: "Na san haka zai faru. Ba zan zauna a cikin gidan nan ba. Wuce wa zan yi, zan bar muku gidan." "Auta, kul! Koma ɗakin ka, ja matar ka ku tafi." Dad ya faɗa cikin fushi da tausayi. Hannun Airah ya ja, suka koma ɗakinsu. "Ya nuna bai son Salma. To ki haƙura mana." "Haba! Ai wannan cin fuska ne." Ta ja jakarta, ta nufi ɗakinta... END. 𝐏𝗿𝗲𝘁𝘁𝘆 𝐒𝐊 Page 60. **************** ************** ___________ "Why? Why?" Zaki ya ja da baya daga in da taron jama’a ya cika wajen. Zuciyarsa cike da rudani, ya buɗe motarsa ya shiga amma ya kasa tuka ta. Ya dafe kansa sannan ya zaro wayarsa ya kira Sk, Pretty a ɗauka bayan bugun biyu. " Wai abin da nake ganin a live, is true?." " Eh Pretty, imagine Rash ya kashe kansa, ga ba ɗaya hujjojin na daga gefan babban motan, sannan ga gawan sa ya ƙone ƙurmus abin ba bu daɗi sam." " Wayyo Allah." " Ina zuwa zan kira ki an jima." daga haka bai ce uffan ba, ya kashe wayar. Ya jingina da kujerar motar yana shakar iskan wake. **************** ************** __________ "Ina alfahari da kai amma waye ka kashe last? na san wani ka kashe." " Wani pastor ne?." Daga haka ya miƙe ya shiga part ɗin sa, da ido ta bisa kawai. yana shiga ɗakin sa ya kwanta kan bed da latsa wayan da ya ciro a cikin aljinun sa, take kiran Skiddo ya shigo bayan ka katse sai ya kira. “Sir, done,” ya faɗa cikin girmamawa. bayan sunyi sallama wa juna. “Good,” "Boss mun god....." “ Enough, Ku tabbatar komai ya taxi nomal kamar yadda na tsara.” “Understood, boss.” Yana kashe wayar ya juya zuwa matasan da suka fi dari uku da ke zaune a wata unguwa ta sirri. Ya ɗaga murya da ƙarfin. “Ku tashi!.” Suka miƙe kamar sojoji. “Yau ƙungiya za ga je huta, da zaran kunji kira to ku amsa, ko wa anan Boss ya zaɓa muku abin da ya da ce, jami'an mu mutane 50, ku an baku hutun sati biyu, mutane 150 wanda Boss ya kuɓutar in ma a prisoner ko a wani gu, duk ya ba ku aikin yi, a ciki akwai mutane 50 wanda ya tura karatu zuwa ƙasar waje, ko dai da nasa a yanzu kuma zamu cika umarnin sa idan har laifuka suka yawaita dole mu dawo, wake tare da ni?." take suka hau faɗin. " Mune! Mune!! Mune!!.". ******************* ****************** Gaba ɗaya wannan babban labarin shike treading a gaba ɗaya yinin jiya da yau, sannan mutane da yawa sun yi farin cikin wannan al'amarin na mutuwan Rash. " Yanzu mai ya kamata mu aikata?" faɗin His Excellent sai Zaki ya ce. " Komai ya ƙare ai, sai dai mu mai fatan alheri sannan Allah ya sa ka mai, ya ce ci ƙasar nan." " Haka ne da bai kashe kansa ba da mu zamu wanke shi a gaban duniya." Meerah ta faɗa ta na gyara kwanciyar Small Ammee, sai Pretty Sk ta ce. " Ba ma wannan ba, shin mai yasa ya ƙona kansa? Why? Da fari mu ma har yanzu bamu da tsayayyen in da za mu sa me sa balle mu ce ko yaga mun sani ne ya gudu, than ba wanda ya san shi balle ace a na neman ransa" " Haka ne maganar ki, amma tin da kowa ya yadda mu ma mubar zan cen kawai." " His Excellent shike nan, bara na ta ka maka." su biyu suka fita sai Meerah ta kalli Sakeenat ta ce. " Yanzu duk wahalar bincikenan ya tashi a banza, koma waye Rash mutum ne na daban gaskiya." " Sosai Maman baby." " Allah ya kyauta." " Ameen ya Allah." ****************** *************** Air Force Base Rayuwan giɗan yanzu sai a hankali kullum cikin rikici ake yi balle da Airah ta kulla ƙawan ce da Fancy, kullum suna tare har school ɗaya suke dan anan A.A ya sanya ta, kamar kullum a sabuwar motan Fancy suka zuwa, yau ma daga schoo suke, bayan sun shiga ciki kowa part ɗin ta ta shiga, Fancy ta fara sauko wa dan neman abin da za ta ci, tana cikin soya plantain sai Airah ta shigo, tare suka kammala sannan suka ci a dining area. Sosai jinin su ya zo ɗaya sannan Fancy na koya mata abubuwa da yawa, Airah ta rasa dalili da ya sa take jin kaman ta san fuskan Fancy a cikin brain ɗin ta amma a duk lokacin da ta matsa a kwakwalwanta akan ta tina sai kanta ya hau ciwo. " Maa ki yadda da ni, ƙawance kawai muke yi amma bana shan........" " Halima shuru ki bari mu shiga ɗaki mana, kin san ba mu kaɗai ba ne." Maa ta faɗa da ɗa ga murya, Part ɗin Maa suka shige, Fancy da ta bisu da ido ta saki ɗan murmushi da bai kai zuci ba, ba dan komai ba sai dan yadda rayuwa ke gwara Maa yanzu, a gun mijinta babu daɗi haka yaran ta sannan su sirikan ta, kuma ga dukkan alamu Halima ma tayo wani tsiyar dan yadda ta ga sun shigo abin ba daɗi. Shuru ne ya ratsa madaidaicin parlourn, a karo na biyu Maa ta kuma sauke ajiyan zuciya ta na kallon Halima wacce take zub da hawaye. " Halima." ta furta cikin sanyi, hakan ya sa Halima ta ɗago jajayen idanunta ta ce " Na'am Maa." " Ki faɗa min gaskiya, shin ke ma kina shaye-shaye kaman Salma sannan da bin maza." " Maa ni ƙawance kaɗai muke yi, ban san ta na wannan halin ba." " Gobe za muje asibiti, fita ki bani guri." da sauri ta bar ɗakin, Maa jin gina kanta ta yi jikin sofa ta na fatan kar ace abin da Salma ke yi ita ma Halima na yi. ********************* ******************* _________ Kwana biyu saboda rasuwan Askira ba ta zuwa gurin aiki domin kullum sai sunje, ta kan kira number Yusuf amma sam ba ta tafiya, yau ta zo aiki kuma tin safe ba ta gan shi ba, ta yanke shawaran in bai zo ba to direct giɗan shi za ta je ta ji shin lafiya. misalin 4:20 suka gama waya da Maa akan an kwantar da Salma, domin rashin lafiya ya ka mata yau, daga zuwa asibi aka ce shan manyan kwayoyi ya huda wasu jangin cikinta, sannan ta na ɗauke da juna biyu. Hankalinta duk ya tashi akan haka, knocking aka yi sai ta ba da permission sannan aka turo ƙafan aka shigo, shin sauri ta miƙa tsaye ta na kallon yusuf da ke sakar mata murmushi. " Wai ina ka shiga ne, My Barrister?." ta tambaye shi ta na gyara vail ɗin abayarta. " Nayi busy ne and wayata tan ya faɗin ne, so sai da na yi welcome back ɗa zu." " Okh, ya kake?" "Steady." ya faɗa ya na ƙarasawa zuwa gaban ta sannan ya miƙa mata file ya ce. "I need ur signature for all this document." Ba tare da ta ce komai ba ta kammala sign din sannan ta miƙa mai amsa ya yi tare ta nufan ƙofa zai fita sai yaji ta ce. "Yusuf." cikin murya mai rauni, zuciyarta na bugawa, ya tsaya ba tare da ya juyo ba. "Ya maganar auren mu ne?."Shiru daga can sai ya ce: "Hafsat... ki bar wannan yanzu. Yunus bashi d lafiya ba na cikin natsuwa." Sai ya fice, yana barin dakin da sauri, zama tayi fuskanta ɗauke da damuwa mara misaltuwa. ****************** ***************** __________ A gidan suka wuni, a tare su ka shiga gidan Sakeenat ta gaidasu Mom sannan suka shiga part ɗin Babban yaya, yau ne karo na farko da Sakeenat ta fara gani Babban yaya, gaishe shi suka yi ya amsa ya na fita daga gidan gaba daya, da gyar Ramlat ta iya fitowa tsaɓar nauyin ciki, gashi ko scanning ba ta zuwa wai ba ta so babu yadda ba'ayi da ita ba, sai dai ta kanje amsan magunguna da wasu kwaje-kwajen. " Ya jikin na ki?." "Alhamdulillah Sakeenat, ya Zaki." " Lpy lau." " Ma sha Allah, barci take yi ne?." ta tambaya ta na kallon Meerah da Small Ammee " Aikam tin ɗazu ta ke yin barci, amma Namesake anya month dion Haihuwan nan bai wuce ba, at least yafi 9 month." " Eh yafi gobe 10 month dai-dai, goben za ni hospital duk da jikina lau ya ke." "To Allah ya raba lafiya, Sakeenat ba ra na barku, mai za ki ci yau?." "Alhamdulillah, yau ki huta, Babban yaya zwi tawomin da shi." daga haka suka yi sallama ta wuce, duk abin Ramlat ke so Meerah na girka mata wani lokacin kuwa su Baby ke mata. a nan ta bar Small Ammee gurin Sakeenat, hira suka sha sosai, can sai Ramlat ta ce. "Wallahi idan ina tare da ke, ƙawata na ke tunawa da rayuwar da muka yi, Allah sarki." " Allah ya bayyana mana ita in dai tana raye, ameen, amma dan Allah Ramlat kin san mahaifiyar ta?." " A'a, amma mahaifiya ta ce, ta santa ta ce ma na, dukka shekaran ta ɗaya 1 kawai ta yi a layin sannan babu wanda ya santa dan ba ta fita, ita ce dai takan leƙa su gaisa, to tin gun haihuwa ta rasu." " Allah sarki na za ci kunyi rayuwa tare ne." " Ko kaɗan, lokacin ni ina jaririya kenan, dan na girma Ramlat ƙarara da wata 1, amma mahaifar mu ta ce, sak Ramlat haka mahaifarta ta ke, kenan sak dai ke, idan na haifa mace ni zan zaɓa sunan idan kuma namiji ne to Babban yaya ne, da ba sunan mu iri ɗaya ba da sunan ƙawata zan sanya, dan ina ƙaunarta sosai." " Ai za ki iya sa wa sai ki sanya nickname mai daɗi kawai." " To, mayyuwa na sanya, Please ki ta yi nemo nickname masu daɗi da ma'ana mana." " Shike nan Auntyn, zan ma duba miki na masoya na haɗa sunan ki da na Babban yaya." " Wai to hakan ya yi amma mai ma'ana" " To ya sunan Babban yaya na gaskiya." " Shuraim." " Nice name." " Uhmmm ai Umar yafi wannan daɗi." Sai da Sakeenat ta yi murmushi sannan ta ce. "A'a gaskiya." Hira suka ɗan kuma yi sannan tayi mata sallama. END. age 61. ******************* *************** _________ Fuskar Malam gaba ɗaya babu annuri, kallonta ya kuma yi ya ce da ita: “Mar’atussaliha, dole gobe mu koma Nigeria. Ƴar auta ta tana asibiti, sannan yara na biyu duk sun haihu, Hajara yaronta ya kai wata biyu, Maryam kuma wata uku, dukkan su maza kuma sunana suka sanya musu, Ina son naje na gansu, Ramlat kuma kwance take, rai a hannun Allah, domin C.S za a yi mata.” Zuciyarta ta buga da sauri, sai dai yanayin Malam ɗin bai mata daɗi ba. A hankali ta buɗe baki ta ce: “Shike nan, amma zamu dawo nan ko?.” “Eh, tunda kina so.” Daga nan suka fara shiri. Ta shiga gidan maƙon ta domin yin sallama da Hajiya. A parlour suka gaisuwa cikin mutunci, kasancewar ba su daɗe da zuwa ƙasar ba. Hajiya kuma ba ta da damuwa sam, sai dai har yau ba su haɗu da ɗanta da kuma sirikarta ba domin kullum suna makaranta. “Allah ya tsare hanya, a gaida kowa idan kin je can,” cewar Hajiya. “In sha Allah Hajiya, ba rana je, dan jirkin safiya zamu bi,” ta amsa da "To madallah" Har haraban gidan Hajiya ta rakota kafin suka rabu. Da ta koma gida ta zauna tana kallon shiri a T.V, sai ga su Yusuf sun shigo. “Hajiya ya gidan?” inji Hasty bayan sun yi sallama. Ta amsa mata tana murmushi. “To ya ya zan yi, ai gobe zan biki ne. Matar da muke ɗan hira da ita gobe za su tafi Nigeria. kinga ba zan zauna ba.” “Allah sarki. Har yau dai ba mu haɗu ba, amma in ta dawo zan je, musamman na gaida ta” Yusuf ya ce yana zama kusa da ita. Hasty ta kalle shi. “Tare zamu yi girki yau da kai fa,” ta faɗa. Shiru yayi sannan ya ce: “Ki huta, ni zan yi kawai.” “Yauwa, thanks.” “To ni ban yadda yarona ya yi girki ba,” Hajiya ta faɗa da sigar wasa. “Uhmm uhmm uhm, ni dai wallahi a’a Hajiya,” Hasty ta furta tana bubbuga ƙafa, ta miƙe ta shige bedroom. Dariya suka sa.. ***************** ***************** FRONTIER CONSULTANT CLINIC ________ zaune yake a ofishinsa yana duba agogo, ya ga saura minti ashirin time ɗin operation. Ya ɗauki waya ya kira lambarta, amma har ya yi miss call uku ba ta ɗaga ba. Daga bi sni sai ga kiran na ta, cikin sauri ya ɗaga. “Ina kika ajiye waya ne? Na san dai yanzu kun koma gida ai.” “Sorry, wanka na shiga yi ne.” “Okay, ya home ɗin?” “Alhamdulillah, Monceur kasan menene?” ta rage murya, kaman me raɗa. “ Sai kin faɗa." "Won’t you scold me if I tell you something?" "No, go ahead. I'm listening." "Earlier when we got back from school, that your sister Barrister, insulted me. Honestly, I don't tolerate disrespect, that’s why I avoid people’s matters, because I have little patience." Sai ta yi shiru shi kuma ya ɗan saki murmushi mara sauti sai ya ce. "What did you do to her?" "I gave her three slaps, then warned her seriously." "Hmm, aren’t you afraid she might retaliate?" "Never. Honey, I’m feeling hungry. Uhmm, I’ll go to the kitchen now." "Okay. I need one peck." "Ummaath. Take care, please.. Bayan kwana ɗaya. ************** *************** “Sir, komai ya kammala. Sign ɗinka kawai ya rage,” ya ajiye wasu takardu. A hankali Haidar ya duba takardun sannan ya sa hannu. Ya ɗago ya kalli saurayin: “Nuruddeen, in the next five minutes, get ready. We're heading to a village near Jaji. Assemble the team and pack the equipment, take everything to its proper place.” “Okay, Sir,” saurayin ya amsa. sannan ya fice, Haidar ya bi shi da ido. Yaron akwai biyayya, ji yake kamar Askira ne babban matsalar shi tun da ya rasu komai ya koma nomal, harta Chul yana mai biyayya da bin tsari ya da komai. Ya ce “Alhamdulillah.” A kullum idan matsala za ta ɓullo, kafin ya yun ƙura sai ya ga an riga an magance ta. ************ ********** Tun da safe ta kammala aikinta, zama ta yi tana duba wani app na sunayen musulci da ma’anarsu, take zuciyarta na raya mata: “Mai zai hana na haɗa sunan Babban Yaya da Ramlat? Sai na samu suna mai daɗi da ganan sai na duba ma'anarsa.” Ta ɗauki takarda, ta rubuta Shuraim da Ramlat. Ta duba haruffa bibbiyu, har sai da ta samu “Shura.” Ta ce, “Shura ai sunan sura ne.” Daga nan ta fara na Ramlat, ta rubuta “RASHU.” Sai ta ce, “Gaskiya bai yi mana ba, bara na cire U.” take ta goge harafin sai idonta ya sauka kan sunan “RASH.” Zaro idanu ta yi, ta kuma kalla. Sai kuma ta dubi Shuraim. Ta haɗa kalmar Rash a cikinsa. Shiru ta yi, sai ta ɗauki wayarta, ta kira Zaki, amma bai ɗauka ba. Nan take kiran Meerah ya shigo, ta ɗauka. “Assalamu alaikum.” “Wa’alaikas salam, Sakeenat. Muna asibiti yanzu, mun samu twins maza daren juya, ki shiga gidanmu ki ku tawo da su Mom da abinci.” “Ma sha Allah! Amma ai da baku faɗa min da wuri...” “Ke dai ki bari. Hankalin mu ya tashi. Yanzu haka jini ake ƙara mata don ta zubar da jini sosai.” “Subhanallah! Ga muna zuwa.” Nan da nan ta shiga gida domin shirya kayan atafiya.. *********** ************ _______ Yau lecture ɗin ya yi zafi sosai. kai ma ciwo yake mata. Ta duba agogon hannunta 10:12am. bai jima ba lectural ɗin ya fita, ko note ɗin ba ta gama ba, ta yi snapping a waya ta fice, ta rasa mai ya sa ko da yaushe sai maza sun tare ta, wasu ko tace tana da aure sai su ƙaryata, kun san farar mace, mai tsayi hmmm sai ma sha Allah, haka yau ma wasu sai da suka tare da bakin class ɗin su, amma ta wuce ta naji suka biyo ta, can kuma suka koma ganin ba za ta kula su ba, can ga hangi Fancy tsaye da wata ƙawarta, ko da ta ƙasa gaisawa suka yi sannan ya shiga mota dan jiran ta, nan da nan Fancy ta shigo motar ta na cewa "Na jiki shiru, a raina na ce, ko Oga bai barki ba ne." " Ai ina shiga class na kira shi, sai ya ce ba bu damuwa." Sai da motan ta hau kan kwalta sannan ta fara gudu, dan so take ta riga su Kandy ganin twins, Meerah ta kira da safe ta ke faɗa mata, ba ɗan text ba da ba ta je ba school ba. *************** ************** _______ Tin a jiya suka iso, sannan giɗansu Zainb ta sa a gyara sosai, hatta girki ta yi musu, bayan sun iso, ita da Muhsin suka je da daddare suka gaidashi Abbuu, da yake yana da mota shiya ɗauko har asibiti a safiyar yau, sannan ya ce an jima zai zo ganin yara ɗan yasan akwai mutane sosai. Babba ne ɗakin haihuwar, Ramlat da barci ya ɗauke ta sannan jinin na ta shiga jikin ta wanda ake ƙara mata, Shuraim ne ya bada na shi, Bayan su shiga gaishe shi su Aunty suka yi ya amsa cikin walwala da ɗan damuwa ganin ƴar sa kwance, jarirai aka bashi ya amsa cikin ƙaunar su, jarirai ne amma kamarsu ɗaya sannan abin Allah komai ɗaya ya yi sai ɗayan ya yi, har ta kwanciya kusan iri ɗaya suke yi, nan fa sai ga su Kandy, Beauty, Beasty, Karis, Butter, Baby da Zubee, Dan har kayansu sun ɗauko wai zasu taya Ramlat raino. Suna da yawa amma babu me magana saboda a na so ta samu hutu, A A ne ya shigo ya kuma duba jikin na ta sannan ya fita, bayan yayi ɗan nisa ya shiga wani ɗakin, Maa, Halima da Hafsat ne ya gani suna zaune jigum-jigum. " Result ya fito ne?" Ya faɗa ya na gyara class ɗin sa sai Maa ta ce. " Nan da 10mnt za mu koma Lab ɗin." Kafin ya ce wani abu Doctor da Salma sun fito daga restroom, kallo ɗaya ya musu ya fice dan bai ma san ganin Salma, shi duk iskan cin da ya yi sai ya ga ta fishi don shi baya neman mata amma ita kam za ta nemi mutum kuma ita ke biya. Zama Salma ta yi da ƙyar dan duk ta fita hayyacinta, ta yi duhu, ga rama da ta yi, Halima duk a tsora ce ta ke akan result domin tana shaye-shaye amma bada yawa ba sannan ita babban ƴar bariki ce, dan ta zub da ciki sau uku ba tare da sanin kowa ba. " Maman Muhammad, kin ga yadda rayuwa ta mai da ni koh?, tuba nake ga Allah babu dare babu rana, hmmm alhaƙi ƙwiƙwiyo ne ga aya ina gani akan rayuwata, domin ni kaina ina ɗauke da ciwon zuciya." "Nasa ni kibar damuwa dan Allah, ki na da ni zan gyara rayuwar ku in sha Allah." "Momyna ki yafe min dan Allah, wallahi na gane kuskure na in sha Allah daga yanzu zan za ma mai miki biyayya." Salma ta kai nan tana rushewa da kuka mai ciwo, hatta Halima sai da hawaye suka zubo mata, ita fatan ta ɗaya ace ba ta ɗauke da HIV dan taga alamomi da yawa na ciwon akan ta. END. Daga alƙalamin pretty SK. [6/12, 1:34] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ If your Mum is alive, may she have a long life to witness your success🤲 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK Page 62 *************** **************** A hankali ta buɗe idanunta, sannan idanun suka sauka akan ledan jinin daya ƙare, ƙoƙarin miƙewa ta ke sai Aunty da Hajiya suka taimaka mata har ta zauna, a hankali ta ke bin ƴan ɗakin da kallo, suna da yawa sosai, a hankali ta kalli maccen da ke kallon ta fuskanta sanye da niƙaf tana mata sannu, sannan ta kalli mahaifinta, murmushin ƙarfin hali ta sakar mai sai ya miƙe ya nufota. " Ramlat ya jikin."  " Abbuu Alhamdulillah." ta faɗa ta na riƙe hannunsa. “I see the babies, may Allah keep you safe and bless them. Two babies are a great blessing from Allah, so be thankful.” “Alhamdulillah. Thank you. When did you arrive?” “Last night. Your mother and I came,” ya faɗa yana nuna Zulaihat, sai ta kalle su ta yi murmushin sannan ta kalli Zainab. " Daure kisha wani abu ƴar nan." Mom wacce ba su jima da zuwa ba ta faɗa. " Momcy ina Sakeenat?." Meerah ta tambaya tana miƙa Hassan gurin Butter. " Muna shigowan haraban asibitin nan, ta ce ta na zuwa wai za ta amso saƙo." "Okay. Baby, do you see how beautiful the babies are?." "How can babies be beautiful? Look at me, am I not beautiful, Aunty?" Karis ta faɗa tana kallon Aunty sai tace "Definitely, my dear niece. Leave them. Even Babban yaya agrees, you’re the most beautiful." "Honestly, not me! If Karis is prettier than me, then I'm in trouble," Beasty ta faɗa take suka kwashe da dariya. Hasty ce ta kira Husty Video call ita ma ta ga yara ma sha Allah, yara wa'inda suka ci Hassan Abdulrahman sai Hussain Abdulraheem dan ɗazu Babban yaya ya raɗa musu, ganin ba ta tashi ba ya sa ya ɗan fita. ****************** ***************** ___________ Tin shigowar su asibitin ta hangi Babban yaya ya na fitowa daga ciki, ta rasa mai yasa yaji ta na son ta ɗan biyeshi dan a tsakanin ɗa zu zuwa yanzu tinanin sa ta ke yi, tasan ba shine Rash ba amma ta na zargin sa. "Momcy ku shiga bara na amso saƙo." ta faɗa haka ta na miƙa ma Mom Basket ɗin hannun ta, amsa suka yi sai ta dinga kallon Babban yaya har ya shiga wata mota, driver daya kawo su ta bashi umarnin ya bi motan da ke gaban sa, cikin kwarewa driver ke bibiyan sa, bayan sun shafe tsawan lokaci suna tafiya har dai ya isa wata unguwa sannan motar ta shiga wani babban gida, sai ta juya ta dawo asibiti, bayan ta sallami driver sannan ta fara ta ka wa haraban asibitin wanda ke da yalwan jama'a. ************* *************** ___________ "Bara na fita na shigo da Fancy wai ba ta gane gurin ba." Meerah ta faɗa sannan ta nufa waje bayan ta ajiye Small Ammee gurin matar Abbuu. *************** *************** ________ "Excuse me, Maa and the others will soon be back, let me quickly check on some patients," Salma replied, without much softness in her voice, tin da aka kwantar da su Momynta ke duba wasu a cikin asibiti, hijab ta sanya sannan ta fita ta na fatan su Maa su dawo daga Lab komai ya tafi nomal. ************* ************** _________ Tin da suka sauka a mota, Airah ta matsa ma Fancy da ta fara rakata gurin A.A, ba yadda ta iya, haka ya sa ta rakata a waje ta tsaya ita kuma Airah ta shiga, a zaune ta gansa ya na aiki a system. " Have you arrived." Be ɗago ba ya furta ɗan ya san tana hanya zuwa. "Yes, I came to get my medicine." "What’s bothering you?" "I feel headache and a little dizzy." He quickly looked at her, standing up in concern. "Subhanallah! Since when have you been feeling like this?." "Uhmmmm, since the morning," ta faɗa tana ƙara sawa kusa da shi. "I’ll take your blood for testing. look at your skin, it’s turning yellow, and your eyes have a bit of redness. now, let me call a nurse..." "Okay, but let me walk Fatima to see the babies. I’ll come back to the test, I think it’s malaria." "Ok you can go?." "Uhmmmm, go ahead, please, take care of yourself." Sai da ya ɗan taka mata sannan ya koma ciki. _______"Sorry sis, I stopped you." ta faɗa tana isa gaban Fancy "No, babu damuwa, yanzu Aunty Meerah nake jira ta fito dan kaimu room din, ya baki medicine ne?." " Wai idan mun gama za'amin text." " Gaskiya kam, dan kin sauya sosai kodai-kodai." tai murmushi ta na shafa cikin na ta. Hannu Meerah ta ɗago musu sai suka isa gunta. " Cewa na yi hawa na uku, amma ina kuka tsaya." " Sorry Aunty duk na ƙosa na gansu, na san su Baby sun iso." " Tin ɗazu ma." suka jera suna hira, bayan sun gaisa da Airah. " Nace ba." a tare suka ƙalla matar da ke magana, ta ke fuskan Meerah ya faɗa ɗa murmushi. " Laa Doctor ina wuni." "Lafiya lau, ina baby girl." "Ta na lafiya, kin dawo nan asibitin ne?." " Eh, waye ba lafiya?." " Uhmn wannan sister tawa ce aka ma C.S, ta haifa twins maza." "Ma sha Allah, wani room ne na zo ganin babies?." " Ai gashi can mujera kawai." daga haka su huɗu suka jera. sai Fancy ta ɗan raɗama Aira "Wannan ce friend ɗin Maa, Doctor, Maman Salma." " Oh, to ba tana idda ba." "Maybe wani abun ne ya kawota nan." _________ Tana tambyan ɗakin haihuwa kenan ta hangi Meerah da Fancy sai wasu, sannan ta hanji in da suka shiga. ******* Cikin jin daɗi da murna, Fancy ta ga yara sannan aka ba Doctor itama ta musu fatan alkairi, Airah da ke tsaye bayan sun gaisa da kowa, brain ɗin ta ya shiga tsalle kaman zai fita, dan mutanen da take gani sai suke mata gizo a cikin kanta, amma ta ɗaure ta zauna. Mama Zulaihat da ke jiran Malam ya dawo su wuce dan ɗakin ya cika da mutane sosai, idonta ne ya kai kan Airah wacce ta kifa kanta akan cinyarta, sai kuma ta mai da kan Zainab da ke mata magana. " Assalamu alaikum." Sakeenat ta faɗa ta na shigowa. " Ke wai ina kika je? Kin san kira na wa Zaki ya miki?." Hajiya ta faɗa ta na miƙa mata wayan ta, sai ta ce " Na ɗan tsaya ne kawai." " Yayi kyau ai kyamai explain, kusan 40mnt da kiran sa." Faɗin Meerah. Doctor ta ɗago kai ta ƙalla Sakeenat, take gabanta ya faɗi ganin wannan yarinyar a karo na biyu, ta nufo ta amsan Hassan ta yi a gun Doctor itama ta na kallonta. " Ya sunanki?." "Sakeenat." ta faɗa ta na zama a gefan ta, Doctor ɗin jikinta a mace yake, jiran Ramlat ta ke dan an ce Momcy na gasa mata a toilet. Jim Sakeenat ta aje wannan ta nufa in da ɗayan jaririn ya ke. "Ɗan na ga Hussain." ba ta kalleta ta fara miƙa mata Hussain ɗin sai dai mai idanunta ne suka kalli yarin yar, a matuƙar tsoro ce ta. da sauri ta miƙe tana ƙare ma Sakeenat kallo, kowa na room ɗin sai kallon ta suke dan yadda ta miƙe ɗin ma abin kallo ne. " Wacece ke." Jin irin tambaya da matar ta yi mata yasa ta miƙa ma Zainab yaron ta ce. "Kin san ni ne?." take ta fizge niƙaf ɗin fuskanta, ba Sakeenat kaɗai ba kowa sai da ya miƙe ganin fuskan Mama Zulaihat, tsayi, kama, skin colour iri ɗaya sai dai ana kallo an san Zulaihat ba yarinya ba ce dan za ta haifa Sakeenat. "Zulaihat." Doctor ta faɗa da ƙarfi mai haɗe da firgice da tsoro, Zulaihat ɗin ta kalli mai magana wanda sai da take tayi baya-baya, Momcy tayi saurin tare ta fe cikin faɗin. "Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un. Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un, innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un.' Doctor Mariya ita ma zaunar da ita a kayi sannan suka kalli juna, ita dai Sakeenat jin gina tai da bango, a karo na biyu ta ga mace mai kama da ita sai. ______ Momcy da Ramlat ne suka fito suna tambyan lafiya, sai a lokacin Airah ta ɗago taga mai ke faruwa dan tini ta yi nisa da tinani, fuskokin uku ta gani a jere, Mama Zulaihat, Sakeenat da Ramlat, ihu ta sa wanda kowa ya mai da ido kanta sai ta tafi luuuu ta faɗi ƙasa. Ana wata ga wata, abu sai addu'a kawai, dan Abbu na shigowa yaga faɗin Airah, shi ya kira Doctor's suka tai maka mata amma ina ta shiga doguwan su, ko da A.A ya ji, hankali ta she ya nufa room ɗin da aka kwantar da ita, abu biyu sun haɗe mai, dan Halima an gano ta na ɗauke da HIV, sannan Maa ta suma amma bata farka sai dai ana sa mata drip.   __  After 1 hour __ Babu mai motsin a ɗakin sai ƙafan fanka da kuka small Ammee, Doctor Mariya ce ta miƙe da ƙyar sannan ta nufi Mama Zulaihat da ta rufe idanunta sai hawaye ke zubowa, durgusawa Doctor ta yi sannan ta haɗe hannunta tana ce wa "Dan Allah ki yafemi, ji nake alhakin ki ne keta bi na, tin ba yau ba nake neman ki amma ban sameki ba, na sani na miki......" Sai kuka ya kwace mata sannan ta ci gaba da ce "A lokacin duniya na ruɗata fiye da tinani mai tinani." kowa dai kallonsu yake yi, sai Abbu ya ce. " Mar'atussaliha me ke faruwa ne? Sam ban gane in da kuka dosa ba, wace ce wannan matar?." sai a lokacin ta ɗago, jajayen idanunta ta kalli Abbu ta ce. "A lokacin auren mu na ɓoyema ai niyin labarin aure na, badan komai ba sai dan ba na so tinawa da wannan rayuwan na har a ba da." Sai ta mai da idonta kan Doctor ta ce "Ban mutu ba, Allah ya yi ina da tsawan rai a gaba." Bara na baka labari na    Labari --------- cikin dare naƙuda ta ya tashi, a napep ɗin maƙocin mu aka kaini wani ƙaramin asibiti, aka bani gado, a dokan su ba'a zama da majinyaci dan haka, Malam (mijina), ya koma gida da niyyan washegari zai tawo da kayayyakina, bai so ta fiya ba amma nurses fin nan suka sa ya wuce, alluran aka min wanda ni kai na ban san na menene ba, haihuwar fari ce ko ya ye ne ina buƙatar wani a kusa dani, ciwo sosai na keji a kowa ni sassa na jiki na, bayan na ɗau lokaci a haka sai na ji muta ne sun shigo, ban shedi su waye ba sai naji suna ce wa. " Doctor Mariya munyi mata alluran sannan mun kwada lafiya lau ta ke." " Yauwa yanzu kuje room 17 Aminity, ki ce ma Hajiya mun samu kidney ɗin, ta shirya tiyata yanzu." da ga nan ban kuma jin su ba sai bayan wani lokaci mai tsayi, na ji na dawo dai-dai amma jikina ya na min ciwo sosai, ko bayan na buɗe idanuna ni kaɗai na gani sannan babu cikin nawa gashi babu motsin kowa a kusa da ni, ta ɓa cikina nayi in da na ga ɗinkin guri biyu, komawa nayi na kwanta dan motsi ma wahala ya kemin, ban san dalilin ba amma ko da wasu suka kuma shigowa na kasa motsi sai dai abin da na ji suna faɗi ya sa na ɗauke wuta " Allah sarki, baiwar Allah nan abin tausayi, gaskiya Doctor Mariya ba ta ɗa tausayi in dai akan kuɗi ne, da wanne za ta ji c.s ko musanya mata kidney." "Nurse Harira abin takaicin ma na wata wacce na ke zatan tafi 50yrs, aka sanya mata." "Duk talauci ne ya kawo haka fa, mijin ya bani tausayi da ya bar nan yana kuka tare da baby a hannu." "Hmmm Allah ya isar mata kawai, amma abu bai yi daɗi ba, mu kan mu muna cikin hatsari dan idan kalma ɗaya ya fita mune." Da ganan sabon hawaye wa gangaromin take na suma bayan na fara, mutane ne uku na gani a biyu da kayan nurses sai ɗaya da kayan gida amma ta sa lab-coat. " Ya jikin." da kai na amsa mata sannan na ji tace "Harira ɗauko wannan injection ɗin P.I.D."  "Okh." har ta kai ƙofa sai ta juyi ta ce "Doctor Mariya P.I.D A1 ko A1q." " A1q." Da ido na bisu sannan a hankali na ce. " Ina mijina?."  "Bai zo ba, sannan ina miki ta'aziyyar ƴar da kika haifa ta koma ga Allah." Rintse ido na yi sannan na ce. "Doctor Mariya koh?." Matar da nake kallo ta ɗaga min kai, sai na ce "ina buƙatar wayana?" "Sorry babu dama ki bari zuwa anjima." Ganin basu da niyyan ba ni wayan sai na yi shiru, daga nan ban kuma farkawa ba sai bayan sati ɗaya, in da na tsinci kai na cikin birnin Saudiyya, gurin wata baiwar Allah, ita ke bani labarin yaron ta ne ya tsinci ni a cikin bola, da yajin ina da rai sai ya tawo da ni Saudiyya, daga nan na ci gaba da rayuwa a can cikin ciwo a haka har aka kai ni asibiti a ka sauyamin sabuwar ƙoda. ***** Sai kuka ya kuma ƙwace mata, a hankali Abbu ya buɗe baki ya ce. " Me ya sa baki nemi mijin ki ba?." " Ta ya zan ne me shi, rayuwan wahala nake yi a gidan, sam bai damu da ni ba, a ce mai na mutu, shine ya tafi da ƴar da muka haifa, ai sai ya nemi gawata ko." Kowa jikin sa yayi sanyi balle Doctor, a hankali ta ce. "Nasan na yi kuskure dan Allah ki yafemin, Please, sannan ina ji a jikina wannan ƴar ki ce." ɗaga ido ta yi ta kalli Sakeenat dake zubar da kwalla, sai a lokacin Sakeenat ta buɗa baki ta ce. "Ni ba ƴar ta ba ce." take ta basu labarin rayuwarta dana Ramlat wacce har yau shiru abu ya kusa rufa shekara. "Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un." Abin da Doctor ta faɗa kenan sannan ta miƙe da ga tsugunne, gaban Sakeenat ta tsaya sai ta janyo ta sannan ta duba hannunta, take wannan tambarin ya bayyana ya ƙara girma da kyau, duk da ta na da duhu amma gashi nan ya yi raɗau, rungume ta tayi ta na cewa. " Wallahi ƴar ki ce wannan, na aikata babban zunubi a rayuwata a cikin manya-manyan shine wannan mugun aikin da na miki, twins mata ki ka haifa, Hassana ta na da wannan alaman a hagu sai Hussaini mai wannan alaman a hannun dama, ni na hana a ba mijinki dukka saboda na san ba zai iya raunon su ba, sai na ba ɗaya daga cikin nurses da ta kai ta gidan marayu, sai dai aka kawo min labarin tayi accident, na zaci har da jaririyan ne ta rasu...." , sai saɓon salati daya cika gurin, take Doctor ta zuɓe a gurin, nan hankali ya kuma ta shi, abu mafi razar da su shine, bayan minti biyar a lokacin da wata Doctor Shamsiya ta sadanar da su rasuwarta Doctor Mariya. ************ ************* _______ Ganin har gitsin ya yi yawa, ya sa duk suka wuce zuwa family house ɗin ƙanƙara, dan abin ya shafi Mama Zulaihat da Sakeenat, sannan ance musu kar kowa ya dawo saboda suna damun mara sa lafiya, nan da kwana uku sai su dawo ɗaukan Ramlat ɗin. ______ Maa suma dare na yi su ka koma gida dan ba ta farfaɗo da wuri ba har ankai ƙawarta makwancinta, rayuwa kenan, duk ciwon da Salma ke ji sai ta ji ta dawo lau dan mutuwan ya dake ta sosai, ta sha kuka kaman ranta zai fita, haka Halima ma. Itama Hafsat da ta dawo da ƙuncin soyayyan Yusuf, gashi Boka ya ce in ba'ayi sa'a ba zai dawo kan ta , to duk a ruɗe take gashi gidan nasu ya hargitse, duk ta shiga damuwa sosai. End. Daga alƙalamin pretty SK. [6/12, 2:46] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ If your Mum is alive, may she have a long life to witness your success🤲 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK Page 63. ************** ************* _____ Fancy ce zaune gefan Airah, sai A.A da ke ƙara duba jikin ta. " Matar Yaya kije gida kawai, ai ina nan karki damu." "A'a ƙanin miji, ni na janyota nan dan Allah ka barni na kwana." "To ai kinga in kika koma da safe sai ki tawo mana da abubuwan da muke buƙata, dan ta shiga doguwar suma, amma wai su waye ta gani ne haka?." ya ƙa ra sa maganan cikin jimami. "To kawai miƙe wa tayi sannan ta yi ihu shike nan, da ya ke muna da yawa bana ce ga wanda ta ga ni ba." "Hmmmm okay." sai ya fita, ba yadda ta iya haka zuwa 10pm, M.d ya zo ya ɗauke ta a motar ta. **************** *************** ____ Nan ma su biyu ne kawai, Ramlat da Meerah dan an yi an yi ta wuce gida Aunty ta zauna ta ƙi yadda, dan haka suka bar ta. " Yanzu fa shike nan Doctor Mariya, Allah sarki, Allah ya jiƙanta da Rahma." "Ameen ya Allah, abu kaman wasa da ka zubewa, takwara wallahi gani nake kaman mafarki, Allah sarki Sakeenat, Allah ke nan." Sai ga hawaye a idonta, sharr sharr, hannu ta sanya ta share sannan ta shiga toilet, da ido Meerah ta bi ta ɗan ta san ta tina Ramkat ne. ************ ************* _____ Tin bayan da suka koma gida kowa ya shiga jimami sosai, sannan aka watse, Kandy,Beauty,Beasty da Zubee su ka wuce gida, dan su Baby sun ƙi binsu, Abbuu shima tafiya suka yi da yamma shi da Mama Zulaihat bayan ta sha rarrashi sosai, haka Sakeenat ma sai da Zaki yazo tukun ya samu ta natsu. **************** ************** SAUDIYYA Hajiya tin 9:00pm ta yi barci, su biyu ne zaune a parlourn suna hira amma hankalinta sam ba ya jikinta domin gida kawai take tinani, gashi matar Boss ta haihu za ta so a yi suna ta nan. " Baby what's wrong?." Sai da ta ɗan firgita dan unexpected ta ji muryan na sa. " Nothing Dear, take your medicine, and start with Bismillah be for you drink." Ta faɗa ta na miƙa mai ruwan zam-zam daya sha addu'oin karya sihiri. amsa ya yi sannan ya yi yadda ta ce ya sha, ya na ga ma wa ya miƙe da niyyan shiga bedroom sai kuma ya zauna yana sakin phone ɗinsa ƙasa sannan ya dafe kansa, yana faman kiran sunan Allah, a ruɗe take tambayan sa. " Dear what happen?". Bai ma san ta nayi ba, addu'a ta fara tofa mai cikin ikon Allah cikin minti biyar sai ya fara atshawa sai da ya yi sau bakwai a jere sannan ya kalleta ya ce. " Menene a cikin kai na wanda yau aka ya ye min, na ji kaman an cire min blanket mai zafi a cikin kai na, wait..... why are you crying." ta san waraka ta zo dan an ce sau uku in kasha an gama, kuka ta fara yi sannan ta shiga ɗakin Hajiya, barci take yi amma Hasty ta fara bubbuga ƙafarta a hankali ta na ce wa. " Hajiya! Hajiya!! Hajiya tah Please wake up, Hajjaju." cikin kuka take magana sai Hajiya ta farka ganin irin kukan da take yasa Hajiya ta watstsake ta na miƙewa sannan ta ce. "Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un, Hassana me ke faruwa? Wa ya mutu? Ko jikin Hassan ne?." ba amsa sai ta rungumeta sannan ta ce. " Hajiya Hassa...." Sai kuma ta yi shuru, amma ganin har Hajiya zuciyarta ta fara bugawa da ƙarfi ya sa kuma ce wa "Alhamdulillah ya samu lafiya, sihirin ya karye Hajiya." " Alhamdulillah, amma shine za ki tsora ta ni haka." "I'm sorry Hajjiyatah." Sai kuma ta saki murmushi, tin shigowar ta yake bayanta, duk yaji zan cen su. A hankali ya ta ko har zuwa gaban su sannan ya ce. " Malama kar ki karyamin tsohuwa ta.". " Uhmmm ai Hajiya ta ce." " A'a sakar min wiyarta haka kawai kin shaƙo min ita." Sai ta sake ta, baki ta turo, Hajiya ta riƙon hannun ta sannan ta ce. "Ƙyale shi, ke ce ƴata ai." " Haba Hajiya to ni fa?." " Tafi ka bani guri, kasan......" Sai hawaye, labarin abin da ya faru aka ba shi duk da akwai wanda yakan sani amma bai san dalilin yin shi ba. Haƙuri ya basu sannan ya ce su shirya jibi za su koma gida. *************** *************** Air Force Base ________ Gaba ɗaya gidan babu daɗi, Maa tana cikin yanayi mara daɗi, ta so a bar mata Salma amma ƴan uwar Doctor Mariya sun tafi da ita Bauchi, gidan sam babu daɗi, ko da Fancy ta dawo ta yi mata gaisuwa ba ta jira mai za ta ce ba ta wuce part ɗin ta dan yanzu ita fatanta Airah ta samu lafiya. Washegari da safe Hafsat na zaune a parlourn ta na latsa waya sai ga Fancy za ta shiga kitchen dan haɗa breakfast, har ta wuce Hafsat sai ta jiyo ta na cewa. " Ki haɗon min lemon tea yanzu." Kamar Fancy za ta tanka sai kawai ta shiga kitchen, haɗa girki ta yi mai rai da lafiya, sannan ta zu ba ruwa a flask, haɗawa ta yi a Basket sannan ta kai motan ta, bayan ta koma kitchen ɗin ta tadda ta Hafsat a ciki ta na buɗe-buɗe. "Lafiya kuwa?." " Lafiyar ce ta kawo haka, ina tea ɗin?." Sai da Fancy ta saki murmushi irin na kin mai da kanki banza. "Wa ki ka haifa? Wa kika aje da zai making tea for you?." "What..?." Hafsat ta riƙo hannunta, fizge hannun ta yi ta na ce wa "Ke dalla gyale ni, ina da aikin yi yanzu, na ga kaman neman rigima ta kike yi, so mind your self." "Hehehehe, who are you?." " Your Aunty." Kafin Hafsat ta kuna mai da magana, ta ji kaman an buga ma ta guduma a kwanyar kanta, ihu ta sanya mai razanarwa ta na toshe kunne, Fancy ba ya ta ja sai kuma ta nufeta ta na ce wa. "Subuhanallah meneme?." Take Maa, Dad da Halima suka shigo a ruɗe dan har lokacin ta na ihu, tin daga kallon da Maa ta yi mata ta ji ajikinta tasan hala ace ta mata wani abu ne. "Fatima me ya sa me ta?." " Dad ni ma ihunta kawai naji." Abin da ta ce kenan sannan ta fita dan basu guri, da ƙyar Hafsat ta yi shuru sai ta ɗauke huta gaba ɗaya, da ƙyar a ka Kaita parlourn, bayan an kwantar da ita, Maa ta ɗibo ruwa aka yayyafa mata duk da idanunta suna buɗe. Dad addu'a ya fara tofa mata, amma ta ƙafe cak. Bayan sun ɗau lokaci a haka, Maa da Halima sun fara kuka, sai ta saki wani ihu sosai wanda yasa suka toshe ƙunnuwan su, take ta miƙe daga kwance ta na bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya, sai ta fashe da dariya mai sautin kuka. " Hahahahaha ni ce, wallahi ni ce, kalli Maa ashe ni ce fa, ke ma taɓani kiji ai ni ce ko?." ta kai nan ta na kallon Halima, Dad ne ya riƙo hannunta ya ce " Hafsat! Hafsat!! Hafsat!!! Are you okay? What's wrong with you?." Sai Hafsat ta kallesa ta ce " Waye kai, na ce kalle ni, ai ni ce ko, ni zan aura shi, wallahi ni ce koh haka Boka ya ce min ai." Salati suka ɗauka ɗan ya tabbata Hafsat hauka ya sa me ta, hatta Fancy wacce ke tsaye jikin step, jikin ta ya yi sanyi sosai. ***************** ***************** Bayan kwana huɗu ______ Yadda kasan ana wani babban shagali ne a gidan, sakamakon dawowan Maman twins, Mutane uku ne suka je suka ɗauko ta, Hajiya, Mama Zulaihat da Karima, ko hour ba suyi ba, suka dawo da ita dan Meerah ta gama haɗa musu komai da suke buƙata, kafin su fito suka leƙa Fancy dan ganin me jiki, sai dai har lokacin ba ta farka ba, suka ma Fancy gaisuwa da fatan ta samu lafiya. Ko bayan sun iso gida kowa sai murya ya ke, part ɗin ta sauka akan ta tadda Hajara, Maryam, da Zainab, farin ciki kaman me agunta, yinin ranan sai hamdala dan kowa yana cikin farin ciki. Bayan kwana biyu _____ Pazar Q, Pazar M, Zaki, Abbu, Mama Zulaikha, Sakeenat sai Hajiya, sune zaune a parlour madaidai ci, bayan ɗan lokaci Maman Rabi ta kawo musu pure water, sannan Baba shima ya fito dan wanka yake yi aka ce yayi baƙi. Koyan sun gaisa aka gabatar mai da dalilin zuwan su, ya yi mamaki ganin Zulaikha na raye amma abu na Allah, kuka ya sha sosai tare da neman yafiyansu, sannan itama Maman ta ne ma tafiya cikin ikon Allah Mama Zulaikha ya tafe tare da musu fatan Alheri. Pazar Q da Zaki suka ma Baba kyuata kuɗi masu yawa sannan suka bar gidan. RASH ______ Zaune yake akan kujera mai juyi sai ya kalli Adamsy ya ce "Ina jinka." taka Adamsy ya buɗe wani babban littafi ya fara magana. "A yadda Spider ya bincika shine, Sunan sa Nura Isma'il, yana da yara biyu maza, matar sa ta rasu tin shekaru uku da suka wuce, yana koyarwa a wata Secondary School anan Barno, ɓata yara mata shine babban aikinsa, doka ba ta aiki akansa sam dan ya na kuɗi da manyan mutane a bayan sa." Sai ya yi shuru, sai Boss ya ce. "Zuwa gobe na ke so aka wo min shi, ba kisa yanzu amma zamu koya mai darasi." Daga haka ya miƙe sanann ya shiga room ɗin sa, Spider da ke kallon Adamsy ya ce. "Dole team ta haɗu nan dan lokaci, dan na ga alama idan ba Rash ya bayyana ba ba za'a dena wanna aikin ba." "Hakane amma kasan ƙasar nan, sai ace za a kama shi ɗan ko a yanzu ne mansa ake." Faɗin Skiddo da ke gyefan su, sai Adamsy ya ce. "Hmmmmm mu na da ƙarfin iko ai, Babu mai iya shiga gonar mu." "Skiddo wai nan mu jami'ai ne koh? da wannan kakin kwanda wannan." Ya faɗa yana nuna tambarin Rash a jikin rigan da ke gyefan sa. "Sosai ma kuwa dan wannan ta ce ƙasar muke..... END Daga alƙalamin pretty SK. [6/12, 12:46] ᑭᖇᗴTTY ՏK ✍️✍️✍️: https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIAION (J.W.A)💪 Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✍️ If your Mum is alive, may she have a long life to witness your success🤲 𝐑𝐀𝐒𝐇 Ɓ𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐄𝐍 𝐌𝐀𝐒𝐇𝐄Ƙ𝐈 ᑭᖇᗴTTY ՏK Page 64. Ranar Suna. _______Gida ya cika sosai, mata kowa ta sha lalle da kitso, haka aka wuni ranan gidan yasha taro, rago shida, shanu biyu aka yanka, Ramlat ta sha kyau sosai, bayan an gama walima zuwa yamma ladies suka baza M.P a cikin gida, sun shashe sosai, amma banda Fancy, dan ita ba ta jima ba ta wuce asibiti, Hasty ma ta zo dan a daren suka dawo dan sun tsaya shirin ne a natse. Zuwa dare duk an watse sai mutan gida, Ladies dai su 8 wai anan zasu kwana gobe za su tafi. Hajara da Maryam suma sun leƙo amma Abbuu tin 5pm ya ce su huce dan duk bayan two days sai sun zo. Doguwar riga less ɗinkin dogan riga ta cire dan sanya masu nauyi, bayan ta sanya mai ɗan sauƙi, ta ɗauki wayarta sabuwa da daren jiya Babban yaya ya sauya mata, kiran shi ta yi amma bai ɗauka ba sai bayan ta aje wayan sai ga kiran shi. "Ina kaje?." "Hmmmmm ko sallama ai kyamin, amma an fara min tambayoyi kaman ɗan yaro, I'm father now." Murmushi ta yi sannan ta ce. "Tom Baban Twins ina kaje, tin 3pm ka bar gidan nan." "Ki ce yanzu kin samin ido, na je wani gu ne." "Ohhh ina ke nan." "Kifayaty zan kira ina zuwa." Kafin ta ce komai ya katse kiran, ita har ranta tasan Shuraim ba zai bar aikin kasada ba amma ta na mai fatan ya de na. ************** *************** Air Force Base _________ Maa ce zaune ta yi jugum tana kallon ƙanana ta Hafsat da Halima, Hafsat hauka kullum gaba yake yi, ita kuma Halima wasu mugayen ƙuraje ne ya fito mata a dukkan jikinta, su na da ƙaiƙayi sosai, ga su sunyi ruwa idan kuma ta fashe akwai azaba sosai, kallon su take cikin son gano shin itace silan wannan yaruwan ta su ko sune, da iyayenta na raye sam ba za su zo ganin wannan lokacin ba, sannan yaranta maza babu mai shiga harkan su, balle Dad da ko ɗaki ba su haɗawa, so ta ke tama kanta karatun ta natsu amma ta rasa ta ina za ta fara. Shurun ne ya katse da shigowan Fancy. "Maa sannu da gida." Ba tare da Maa ta amsa ba Fancy ta wuce, da idanu ta bi ta tana mai son gano ai bunta amma ta kasa, Hafsat ce ta mike tsaye tana sosa kanta wanda duk ya hauka ce. "Ke ina zuwa?." Sai ta kwashe da dariya ta na daka tsalle da hayewa stairs, Halima idanu ta buɗe idanu da ƙyar sannan ta ce. "Maa." Da sauri ma ta nufeta ta na cewa "Halima menene, me ke damunki?." "Maa ki ya femin mutuwa zan...." "Kul Halima in sha Allah za ki samu lafiya kinji." Sai ga hawaye sun wanke mata fuska, sai ga Da sun shigo shida A.A, bayan sun shigo sai ga wasu mutane a bayan su. "Baban Muhammad kalli Halima, wayyo Allah na ban san ta mutu." "Yi shuru, Maa kin yadda da ƙaddara ko a'a." cikin kuka ta ce. "Na yadda." "To muje." Kafin ta kuma magana ya ja hannunta suka shige part ɗin su, A.A dake tsaye jikinsa a mace ya ce. "Wannan ce mara lafiyan, ku ɗauke ta." Wasu mata suka dauki Halima akan wani gado, ta so tayi magana amma ta kasa sai hawaye kawai, take M.d ya sauko riƙe da hannun Hafsat, yana isowa ya ce. " Ga ta." nan ma wasu suka riketa suka yi waje da ita. " Allah ya sa a da ce." " Ameen brother, Halima na ta ne guarantee." "Hmmmmm Allah sarki rayuwa, ya jikin matarka, ɗazu na shigo a kace ka fita." " Jiki Alhamdulillah." _______ Dad ya kalli Maa ya ce "Muna sane da halin yaran nan, sai muka sa miki ido, domin kisan irin isharan da Allah ya musu, kina dai kallo kuma kina saurare, rayuwa sam ba gurin dawwama ba ce, ke sheda ce a yau ina ƙawarki Mariya, ba ta duniya, ke kanki baki fi ƙarfin Allah ya ɗauki ki yanzu ba." Sai ya nisa sannan ya da sa. " Aboki na tin na yarinta Askira, tin daga mutuwar sa ya gane hanyar da nabi, Allah ya so ni da rahma, ke ma haka amma kin ba sar neman shiga wata halakar kike, dan Allah ki natsu kisan abin da ya dace ki yi." "Kai co na Bababn Muhammad, wallahi na tuba na bi Allah." Sai ta fashe da kuka, rungume ta ya yi ya na ce wa. " Is okay, by now ki san me ya dace ki yi a rayuwa, and kin yadda da mijinki?." Da daga mai kai sai ya da sa da ce wa "Ban san ki tambaya ina Hafsat da Halima suke, dan yanzu ba sa gidan nan, amma da sa ni na kuma da yadda ta, kin san ba zan cutar da su ba, dan nima ƙannai na ne kuma yara na." "Ina ka kaisu toh?." " Kimin alƙawarin ba za ki tambaya kowa ba kuma ni ma kibar tambaya ta, lokaci na nan zuwa za su dawo." "Shike nan na yadda." END. Page 65. *********** ************ _____ Da idanu ta bisa har ya isa wardrobe ya sanya kayan aikin sa, sannan ya juyo ya kalleta. " Wannan kallon fa, ko duk gajiyan suna ne?." "Sai ka ce Naman twins." "To ai naga duk kin gaji ne, kuma nima twins nake so gaskiya." Ya faɗa ya na ɗago fuskanta sai ta sakar mai da murmushi, sannan ta ce. " Allah ya ba mu." "Ameen Mu Pretty Sk, faɗa min ko a kunne ne?." " Me ne?." Ta mai tambayan tana gyara zaman ta zuwa jikinsa. "Kullum ƙara kyau ki ke yi, menene sirrin ne?." Dariya ta ɗan yi tana aiyana ta yadda za ta sanya ya faɗa mata abun da ta ke maradi. " Kai ne sirrin ai, kana kula da ni sosai, sai dai na ce Alhamdulillah, Baby na Dan Allah ka faɗamin wani abu mana." "Ina jinki." "Waye ya tona asirina har kuka kama ni?." " Oh Pretty Sk abu baya wuce a gunki wai......" "uhm uhm uhm uhm." "A'a ni kar kimin shaƙwaɓa ki hani fita, i promise idan na dawo zan faɗa miki." Murmushi ta yi sannan ta mike tsaye, tare suka yi breakfast sanna ya wuce, sai misalin 10am ta shiga gidan suna dan yin aiki, a parlour ta haɗu da Meerah, part ɗin ta suka shiga dan kaso wasu kaya. Wanke kayan cikin nama suke yi su, Beauty,Kandy, Sakeenat da Meerah, su kuma Beasty,Hasty, da Husty suna yankan nama ne. "Bayan Fatima sai waye mai juna biyu a cikin ku, shurun ya yi yawa fa." Meerah ta faɗa sai suka kwashe da dariya. "Beasty, Hasty, da Husty Allah ya basu saura mu." Faɗin Kandy sai Beasty ta ce. "A'a ba dai ni ba ko?" "Ke mana." "Ai kema kina da shi." Beauty ta dalla ma Beasty hararan wasa, sai Meerah ta ce " To menene abin jin kunya dukkan mu mata ne ai, Allah dai ya raba lafiya." "Ameen" suka haɗa baki sai Meerah ta kuma ce wa. " Kyanshi Hasty da Husty ku haifo twins rana ɗaya." "Wallahi kam." "Su kandy an iya bada amsa ai, saura ke da Sk ai." Sakeenat dai murmushi ta yi dan calculation ta ke yi, a yau ta ke so jin labarin Baban yaya a baki mutane hudu, Zaki, Ramlat, team of ladies da Meerah. "Auntyn Meerah, ki ba mu labarin soyayyan ku da His Excellency, dan jiya munga love." Dariya suka sa sai Hasty ta ce. " Gaskiya kam a bamu labari." "Beauty ku gyara na dinga hangen Ummee ammee da kyau." " To uwar son story." Beauty ta faɗa sai Meerah ta ce. "Gaskiya ni bamuyi wani soyayya ba dan ban iya ba, shi kuma Yayanku Haidar, lallaɓa ni yake yi, sai bayan munyi aure ne muka sha love, wata dai ta ba mu na ta." " Da Fancy na nan ne toh da ta bamu dan ita uwar love ce." Faɗin Hasty sai Meerah ta ce. "Naman tweens ba tanan da ita ma ta bamu labari......." "Tab Baban yaya ina ya iya soyayya, hatta abokinsa ba ya bari mu wani sha love balle shi ace yanayi." "Kai Kandy, ai irinsu wallahi sunfi iya soyayya." Sakeenat ta saki murmushi dan anzo in da ta ke so. " Ku dai barshi da sanin System." Faɗin Husty sai Beauty ta ce. "Ke dai bari, ai wannan yadda ku kasan al'jani, da munyi abu take ya ke sani." "Sai na tina rayuwar baya, kaman fa ya dasa mana bi diddigi, komai mukai take ya ke sani, hmmmmm munji jiki wallahi." Husty ta kaina tana tina da yadda suka kwashe da Babban yaya. Sai Sakeenat ta ce. " Kunji daɗi kam, dan samun mai kula da mutum haka ai da daɗi...." " Banda kalan na Baban yaya, dan dai baki san shi bane Aunty Sk, wallahi mun ci uban mu, ai Baban yaya Boss ne, shi yasa muke ce mai Boss." "Kandy ina ranan da kika je birthday ɗin class mate ɗinkin...." "Beauty bar tina min, hmmmm abu kaman wasa yanzu komai ya wuce." "Haka ne, komai lokaci ne ai." Sakeenat ta faɗa bayan ta gama auna zancen su akan mizaji. Bayan sun kammala Sakeenat da Meerah suka je part ɗin Meerah dan duba Small Ammee ko ta farka, ba ta farka ba dan haka suka zauna dan su huta. " Auntyn Meerah wai da gaske haka Babban yaya ya ke, na ganshi kaman ba zai yi zafi ba." " Hmmmm be da zafi amma akwai tsauri akan ladies, yadda Haidar ke faɗa min ya ce sam be damuwa, matsalan sa ɗaya shine rashin zaman gida, yau yana nan gobe ya bar gun." "Wai maybe yana yin work na shi ne?". Sk ta furta da fatan ta samu ƙarin bayani agunta. "Eh to online business da aikin bank yake yi, na san dai zai zama mai matsayi because ya san system sosai." Daga nan suka can za hira zuwa wani daban. Bayan ɗan lokaci suka koma bakin aiki. Hajiya ce ta ɗauki yaji da ke cikin ƙaramin farin rober ta ce. " Sasakee, ungo wannan ɗan kai ma Me jego." Murmushi ta yi dan jin yadda ta kira ta don ita ce kadai mai kiranta da haka, amsa tayi sanan ta nufa part ɗin Babban yaya, ko bayyan ta ba Ramlat ɗin sai ta ɗauki Hussain tana kallon sa. "Wancan ya fi wannan son barci, duk time ɗin da na leƙo wannan idonsa biyu na ke gani." " Haka suke dan ma bai yawan kuka da abin ba sauƙi." "Aunty Ramlat kin san wai har yanzu wannan mugun na raye, yanzu na tina zan koma gidan na duba wani abu akan sa." Ta kai nan tana kallon fuskan Ramlat da ke latsa waya, yadda ta yi fata ne sai ta ga yana yinta ya sauya sannan ta ce. "Wai Rash?." "Abin da mamaki ko." " Sosai ma kuwa, amma ta ya kuka sani?." "Bincike dai, amma ba Rash ba fa, wani ne Harun da muke bincike a kansa, ɓarawo ne so an ce ya mutu ashe ƙarya ne." Take ta ɗan saki ran ta sanan ta ce. "Wayyo, ai na za ci Rash ne, Allah ya shirya mu gana ɗaya." " Ameen, Bara na koma kar suce na tsaya." Daga haka ta miƙa mata shi sannan ta fice.. **************** ***************** Misalin 4:23pm, a hankali ta fara buɗe idanunta, p.o.p shine abin da idanunta suka fara gani sai ta kalla gefe da gefan ɗakin, Fancy fa ke zaune ta miƙa tare da nufota ta na ce wa. "Alhamdulillah, Alhamdulillah kin farka, Airah sannu ya jikin?." ta faɗa tana taimaka mata ta zauna da kyau. " Bara na kira Doc....." Ta katse magana ta sakamakon riƙo hannunta ta karfi Airah ta yi, sannan ta fara magana a natse kuma a hankali irin na marasa lafiya. "No need, ki kaini gun Ramlat yanzu." "A'a, Doctor zan kira ya ga kin fark...." "Fatima Please, muje yanzu akwai abin da zan ce mata ne." "Ba ki da lafiya, a ina ma kika san ta." "Bazan iya magana ba kawai yanzu dan Allah." Take hawaye suka wanke fuskanta, cikin matuƙar da burgewa Fancy ta rungumeta sannan ta ce. "Mu je." Da ka ganta kasan ba ta cikin isasshen lafiya, dan tafiya ma da ƙyar da take yi, a haka su lallaɓa har haraban Asibitin in da Fancy ta yi parking motarta, ko bayan sun shiga ga ɗau hanya kuka mai ciwo Airah take yi wanda ya yi mugun ba Fancy mamaki, Fancy Kan ta fita ta kira number A.A ta ce mai ya biyo bayan su. Ko a lokacin da ya fito da mamaki yaga sun shiga mota har ta bar asibitin cikin sauri ya sauka daga stairs sannan ya shiga na sa mota tare da kiran Fancy amma ba ta ɗaga ba, har kira biyar ya yi sai ya haƙura tare da ci gaba da bin su. END Page 67. *************** *************** RASH ______________ Shuraim da Adamsy ne suka sauka a mota, a hankali Adam ya ke tura shi a keke ya na mai magana cikin raɗa-raɗa. "Boss, a halin yanzu Spider ya isa can, ya ce tawaga ta zama cikin shiri." "Ku yi komai yadda ya da ce, zuwa 5pm zamu fita." "Okh sir." Tin daga ne sa ƴam matan suka yo kan Babban yaya, Kandy kuma ta ƙarasa kusa da Adam suna ɗan hira, Sakeenat da ke kusa da Meerah kallon su kawai suke kowa da abin da take aiyanawa a ranta. "Baby kira Auntyn ku kice ta zo muyi hotan tarihi da babies." Babban yaya ya faɗa take Baby ta yi cikin gidan dan cika umarnin sa, ba su ɗau lokaci ba sai ga Ramlat ta fito sanye da cikin wani lifaya ja mai kwalliyan ɓaki, kusan ja yana haske fararen mata, take ta haska gurin dan ba ƙarya Ramlat akwai kyau mai suna kyau. Adam ne ya ɗauke su hoto harda su Aunty duk sun fito, hatta Mama Zulaikha ta zo yau ma. Bayan sun gama ne aka koma videos cikin raha suke komai. sec 1, sec 2, sec 3 zuwa sec 10, take get ɗin gidan ya buɗe motoci uku suka shigo haraban gidan, sannan mai gadi ya kulle get ɗin. Kowa ya bi motocin da ido dan ganin su waye a ciki, A.A da ya fi han zari ko motan bai kashe ba ya fito yana nufan motan Fancy da take son daidaita parking ɗin ta, a parking lot sai ɗayan motan ba ban san ta waye ba.................... (Hmmmmm bara mu ɗan huta koh, kaman duk mun gaji.............). ***************** ***************** Air Force Base _________ Shuru babu mai motsi acikin su biyar ɗin da ke parlour, Dad wanda yake gun aiki aka kira shi ya dawo, Maa da ke zaune ta yi tagumi, Hajiya, Yunus da Yusuf suma suna zaune sunyi jugum, dan sun zo ne akan suga Hafsat sai suka riski mummunan labarin da ya sa me ta, ba musu suka yafe mata, Maa ta sha kuka akan haka dan gani ta ke koma menene laifin ta ne akan kabarin Hafsat. "Allah ya kyauta, kuma ya yafe mana gana ɗaya, bara mu ta fi." Hajiya ta faɗa tana miƙawa, su ma twins haka, sai Dad ya ce. "Mun gode Hajiya, Allah ya sa ka da alkhari, mun gode sosai." "Ayya babu da muwa." Har Motan suka raka su, bayan sun koma cikin gida, Maa ta ɗauki wayan Hafsat ɗin tare da cire sim ɗin ta ɓalla, tinda hauka ya sami Hafsat take riƙe da wayarta, ɗazu kam a kaita kira Allah ya so ta ɗauka, ita ce ta musu kwatance gidan bayan sunyi waya da jami'an bakin get base shine suka samu damar shiga..... ____ "Wannan unguwa akwai kyau, ga tsaro ɗan ko ina ga sojoji nan." Hajiya ta faɗa a daidai suna barin cikin base ɗin. "Aifa ai su a security suke, yanzu Milinium muka nufa koh?." Yunus ya tambaya dan shi ke driving sai Hajiya ta ce. "Eh, kaimu muga yara, Hassan." "Na'am." Yusuf ya faɗa ya na maida hankalin sa ga su ɗan waya yake latsawa, shi kuma Yunus ya juya kan motansa zuwa gidan su Babynsa. "Karka sa abu a ranka fa, dan Allah komai ya wuce." "Hajiya wallahi ya wuce, da ta na nan ne to sai mun shiga coat, ta sanni ta san waye ni, amma by now ya wuce." "Yauwa yaro na." ****************** ************** Hajiya da Twins ne suka fito a cikin motan dake bayan na A.A, ya tare hanya babu daman su gyara na su parking ɗin dan haka suka fito, ganin jama'a gidan suna tsakar gida ya sa suka nufe so da fara'a. Kafin su fara gaisawa Fancy ta fito daga motarta tana ƙoƙarin zagayawa ɗaukan ɓangaren dan taimaka ma Airah. "Matar Yaya lafiya waina." A.A ya faɗa yana isa gabanta. "Kwada da kazo taimaka ta fito daga cikin motan, ta bi ta ruɗani da na kawota nan gidan." Ta faɗa tana buɗe murfin motan baya dan anan ta Airah ta kwanta. Ganin kaman ba lafiya ba yasa su ka ɗan matsa kusa da Fancy suna tambayan lafiya. "Airah mun zo ki fito." Fancy ta faɗa sai ga Airah ta fito, da fuskan A.A ta fara cin karo take fuskanta ta ƙare haɗewa, hannunta A.A ya rige ya na ce wa. "Airah, lafiya wai? Jikin ki babu kwari, muje na maidaki hosbit......" Hannunta ta fizge tana ce wa "Waye kai? Kyaleni." "Waye, waye ni....." Ya faɗa da wani irin murya dan ya harbo jirgin, Airah ta warke daga cutar da ya ka mata. Kafin ya kuma magana ta nufa Ramlat da gudu ta rungumeta tana kuka ta na ce wa. "Ra...ra..ramm..lat, Ramlat....." Sai luuu ta suma, take suka hau salati, da gyara aka ɗauke ta aka cikin gidan ta ida, A.A dai mutuwar tsaye ya yi, Fancy da Ramlat su ma kaman jikin su ya mutu murus da sauran mutanen da ke tsaye. "Kifayaty kin santa ne?." "A'a, ni ta tsora ta ni wallahi, Allah yasa lafiya dai." Ramlat ta faɗa tana tura Babban yaya zuwa cikin parlour. _______ "Ƙanin miji mu je ciki." Fancy ta faɗa tana yin gaba, take ya bi bayanta, sai dai shi bai ƙarasa cikin babban parlourn ba ya tsaya cak, badan komai ba, sai dan ganin.................... (Kar naja rai koh 🤗 .) ______ sai dan ganin......... Alƙalamina ya karye gaskiya ✍️, Bara na siyo sabo....... Bye guys. Karku manta kuna tare da Pretty SK ce ✍️✍️✍️✍️✍️. Page 68. *********************** ******************** ____________ Fuskoki biyu ya gani a guri ɗaya, saurin da fa kansa ya yi tare da furta duk kalmomin da ke bakin sa, "Lokaci ya yi." Ya furta a hankali yana ƙara ta ku zuwa in da zai zauna, gana ɗaya ya rasa sukuni sai faman bin su yake da idanu, Mama Zulaikha da Sakeenat, ba ma wacce yafi kallo kaman Sakeenat, dafa kansa yayi yana ƙaro dauriya. _______ an samu ta farka da salati a bakinta, A.A shine kan gaba a gurin ɗagota daga kwanciyan, dan ya za ci ta koma gidan jiya ne. "Airah, baki da lafiya, muje asibiti yanzu." "Malam waye kai? Bar ta ɓamin hannu." Ta fizge hannunta sai Fancy ta ce. "Airah wannan Mijin ki ne, Abdullahi ne....." "Fatima." Ta faɗa tana miƙewa tare da nufan Ramlat da duk motsin Airah ta sa ma ido. 'Ramlat na dawo, Ramlat ɗinkin ta dawo, ƙawata ko baki gane ni bane." Ganin Ramlat bata motsa ba ya sa ta sake ta ta nufa Sakeenat ta na kuma ce wa. "Uhmmm ya na sunan ki, ku kalla ko muna da banbanci, ke ma baki ga ne ni ba, yauwa Sakeenat, eh Sakeenat sunan ki koh." Sk ta daga kai kawai batan ta fahimci inda maganar na ta ke dosa ba. "Naga kowa na bina da ido ne, wai lafiya kuwa kumin baya ni na gane." Ta durgushe a ƙasa tana kuka, kowa dai ido ya sa mata, A.A ne ya nufe ta ya ɗagota yana ce wa. "Airah, natsu na ce ki...." "Waye kai?, Waye kai?, Kar ka kuma ta ɓani na faɗa maka." " Ko dai ta samu matsala ne a kanta?." Fancy ta faɗa cikin ɗan da burce wa take, His Excellency da Zaki suka shigo cikin main parlour ɗin, komai ya mai da idon sa ga su, take Airah ta nufi Zaki da gudu ta rungumesa ta na cewa. "Idan kowa ya manta ni, nasan banda kai Mu A. Asad." da sauri ya raba jikin sa da na ta yana kallonta cikin mamaki, duk da A. Asad da ta faɗa ya shiga brain ɗin sa ya ce. "Ki na hauka ne za ki ta ɓani haka, wace ce ke?." Dam Dam, ƙijinta ya buga, baya ta ja sannan ta ɗurƙushe gwiwowinta ta kafin ta fara magana taji an dafa kafaɗarta cikin sauri ta ɗago, sai suka haɗa ido da Ramlat. " Miƙa tsaye, share hawayen ki, faɗa min a ina kika sanni?." Take kanta ya kuma sarawa sai ta dafe kan, Ramlat hannunta ta sa ta riƙon hannunta, take Airah ta kalla hannunta, a kallo ɗaya ƙirjinta ya yi mugun bugawa badan komai ba sai dan kallon hannunsu a tare da ta yi, komai kaman gizo ya ke mata, hannunta ta fizge da ƙarfi ta na kallon hannuta sannan ta janye hannunun rigarta ta na kallo take ta kalla ƙafarta nan ba ba ƙarya gani tai ta fi Ramlat haske, dan haske na ta ba ma irin na Nigeria ba ne, ita da tasan kanta a Black colour. Babu wanda ya kuma magana sai kallonta ake yi da mamakin gaske, nema neme ta shiga yi a parlour ta na ko hangan mirror ta nufa tana kallon kanta, a kallo ɗaya sak da ta dafa ƙirjinta dan ganin halitta ta sauya fiye da tinani. "Airah, wai lafiyan ki kuwa? Me ke faruwa ne?." Fancy ta faɗa kamar ta yi kuka, sai Airah ta kalleta ta ce. "Fancy dole ku ka sa ga ne ni, ni kaina ban gane kai na ba, jibi jikina ya canza, dan Allah wa zai min bayani, kaina kai....kaina...." Take ta kuma zuɓewa a jikin Fancy. Innalillahi wa'inna ilaiyi raji'un. Bayan hours 1 ɗaya. ************** ************** ____________ A firgice ta buɗe idanunta tana kiran sunan Allah, sai ta ji an da fata, kallon wacce ke gefan ta tayi 'Ramlat' take ta sakar mata murmushi, ba ɗan drib ɗin hannunta ba da ta rungume ta, sai tai ta ɗaga mata hannu, Ramlat ta miƙa sannan ta zauna a gyefan gadon ta na ce wa. " Sannu ya jikin?." "Alhamdulillah, Pure white! What is happening to me? Why has my skin changed from black to this?" Ta faɗa tana nuna hannunta da jikinta. "That's enough, my head is already stressed. Are you trying to say you're Ramlat?"* *"Hmmm, my namesake... I can't remember anything clearly. Please, where is my aunt that looks like Rabi? And my father? I know they'll recognize me. Take me to them. The only thing I remember is the car I boarded yesterday on my way to Mama's family’s wedding. Do you know what happened to my skin?" Ta faɗa tana nuna hannunta." "Ramlat ina kika shiga ne tsawon lokaci mai yawa? Sam na kasa yadda wai ke ce, sam babu alaman da ya nuna ke ce, amma naji a raina ke ce, ina zuwa." Ta furta ta na miƙewa tsaye sannan ta fita daga room ɗin, sai a lokacin Airah ta ga ne ashe asibiti ne, ba ta jima da fita sai ga ta ita da ƴan gidan su, sannan da wanda a kallo ɗaya ta ji sam ta tsane sa balle da yake yawan taɓa mata jiki. Idon ta ne suka sauka akan Sakeenat sai hawaye ya gangaro daga idanunta, gyara zama tayi sannan Fancy ta ce. "Ƙanin miji ka mata bayani, kan mu a kulle ya ke sosai, kai ne kawai za ka iya warware wannan case ɗin, sam cikin mu ba musan mene faruwa ba." Shuru yayi sanann ya ɗan taka zuwa gabanta sai ya furta. "Airah, Monceur ɗin kine fa....." "Waye kai Please?." Ta kuma wurga mai tambayan tana mai da kanta ga Sakeenat da ke tsaye gefan wata mai maka da ita again, shuru ta yi dan shine abin da zai fi mata akan ta yi magana. "Airah wannan Mijin ki ne fa." Faɗin Fancy bayan ɗakin ya ɗau shuru. "Miji, Fancy wai hauka kike ko me, wait natina ashe Fancy ce, Uhmmm Hasty da Husty na san ku kuna sona ai, ba kwa ƙyamata Please ku fitar da ni a cikin duhu dan Allah." Ganin idan bashi ba, ba bu mai warware wannan case ɗin, kafin ya furta wani abu sai Aunty ta ce. "Doctor Abdullahi, me ke faruwa, wace ce Airah? A ina kasanta? ta ce ita ce Ramlat ɗin mu, Please ka ma explain ko ka faɗa in da iyayen ta suke da mu nemo su, mu kuma ku koma gida." "Gaskiya zancen ki, ke Fancy a ina kika santa?." Fancy ta kalla Momcy tukun ta ce. "Matar shi ce." Ta faɗa tana nuna A.A. "Muna jinka a ina ne gidan su Airah." "Ya isa, wannan dai da kuke gani itace Ramlat ɗin da kuke magana, ita ce dai sak wancan yarinya, ita ce dai." Ya kaina ya na nuna Sakeenat............. END Page 69. ****************** ************* _____________ "Bara na baku ainihin labarin wanne A.A da wace ce Airah." A.A ya faɗa yana mai fargaban kar Airah ta dena son shi, amma bara dai ya gama faɗi. Kowa shuru ya yi dan ya na son yaji labarin, duk su 10 ne, Ramlat, Fancy, Aunty, A.A, Husty, Hasty, Sakeenat, Mama Zulaikha da Momcy, sauran sun zauna a gida. Labari na A.A - Abdullahi Anas chul, haifaffen ɗan Kaduna ne, Ni ne ƙarami gun iyayena, na taso cikin gata sangarta da wadata, Mahaifiya ta wato Maa, ta sangartan da ni fiye da misali, ban damu da ilimin addini ba sam duk da ina zuwa saboda Yayana Muhammad dake tilasta min akan naje, ni mutun ne mai son shagala da duniya, yau ni ne wannan club ɗin gobe wannan, nakan sha shisha da giya wani lokacin, ban taɓa na daman wani abu ba saboda iyayena sun tsayamin, amma ban taɓa zina tinda nake, a baya ban taɓa tsammanin akwai ranan da Ni zan faɗa soyayya, dan ni ban kula ko wacce mace. A qata rana bayan na sha nayi ta tul, na shiga mota ta dan na koma gida daga club, a hanya ta wani babban iftila'i ya faru dan accident ɗin da ban taɓa gani ba na ci karo da shi......." Sai ya yi shuru tare da kallon Airah wacce itama ta zuba mai idanu kaman sauran mutan ciki. Ci gaba da magana ya yi cikin taushin halin sa. " Banyi au ne ba, wasu matasa sun tawo a cikin napep ga gudu, nima na danno gudu, haka wata babban mota ma haka, ba na ce nasan me ya faru ba dan ban cikin hayyaci na, na wayi gari ne na ganni a wani ɗan garamin gida, bacin na miƙa tsaye da ta hangi rigata a gyefe guda na sanya sanann na fita waje, wani ɗan dattijo na su zaune a tsakar gidan, da ganina ya miƙe tsaye ya na mun Barka da fitowa. Bayan na natsu ya bani labarin hatsari ne ya kafku sosai, ni da mata ne kawai iska ya kaɗamu wani gangare hanyar da ya sada ƙauye su, shi ya tsince mu sannan ya kawo mu nan dan ba mu kulawa, ashe har kwana biyu nai a doguwar suma, bayan matarsa ta dawo shine ta kaini ɗakin wacce suka kira da Mata ta, hankali ya mugun tashi da na ga yadda da take, ba tare da tinanin komai ba na ɗauke ta d taimakawan su nafita da ga wannan unguwan, na kaita Asibitin mai kyau, bayan kwaje-kwaje aka ce sai an mata aiki dan gefan fuskanta ya lalace, daga ƙasar waje aka zo aka wanann aiki daga bi sani na kaita aka sauya mata fuska sannan aka bata wasu ƙwaya wanda take mutum kan sauya kala, haka akai mata aiki a brain, 8 month tana kwance ina jinya ta....." Sai ya tsagaita tare da kuma kallonta, sam ba zai iya karanta komai dan gane da ita ba. Sai kawai ya da sa. "Tin bayan ranan da nakaita asibiti wallahi wallahi ban taɓa jin ina son ka sance da kowa ba sai ita kawai naji na kamu da soyayyarta, dan haka da na koma gidan wannan Baba na faɗa mai ni ban santa ba amma ina son na taimaka mata, take yace to na aurenta, na ce bansan ko da auren wani a kanta ba, haka dai muka tsaida musu, a ranan aka ɗauramin aure da ita bayan na biya sadaki, domin gasgata ni ga ma su nan." Yana faɗin haka sai ga bayin Allah nan sun shigo, ƙara jaddara magarsa suka yi, da gode ma A.A dan ya maimake su sosai, yanzu haka yaran shi maza biyu ɗaya yana karatu ɗaya kuma ya samar mai aikin soja, kuma sun bar gidan nan ya musu sabo. Baban ne ya faɗa haka. " Ko bayan faruwar abin jami'ai sunyi bincike a in da aka ce wasu matasa sun sake wata budurwa sai tsutsayin ya afku. Duk sun mutu, su biyu Allah ya tsaratar.." "Mama wannan itama ƴar ki ce." Sakeenat ta faɗa tana isa gaban Airah, sai ta rungumeta, tana kuka. "Ramlat ashe mu twins ne, ashe....." "Sakeenat ba a nan ba, ki bari ta samu hutu Please." Aunty ta katseta da faɗin. Ramlat da hannunta ke cikin na Airah ta ƙara matsawa tare da sumbatar shi. Mama Zulaikha itama ta matso ta rungume Airah wacce ake ce ita ta haife ta, tayi ko kwanto kafin ga rungume ta amma bayan ta rungume ta take ta gasgata ƴar tace sai ka ta da ga wannan ta bon a hannunta haka kuma ga wani abu a saitin wiyarta sak irin na ta, safan gun tayi ta sake rungume abarta. *************** *************** 7:30pm suka dawo gida, anan Mama Zulaikha ta ga Hajiya wacce sam ba su haɗu ba, sun yi murna da ganin juna haka haka taga sirikarta harda yaranta twins, wanda suka dawo bayan magrib dan su wuce. Allah ke nan sam ba ta kawo nan kusa zasu haɗu ba sai gashi. Kafin Pazars su dawo ko wacce ta wuce zuwa gidan ta, Mama Zulaikha itama ta wuce da Abbuu ya zo ɗaukan ta, ta so Airah ta bi ta amma Ramlat ta ƙi yadda. hatta Meerah ta yi farin ciki da bayyana Ramlat ɗin. A part ɗin Baban Yaya suka raba ɗare kafin Meerah da Sakeenat suka bar gidan. suna fita Airah ta kalla Ramlat ta ce. " Pure white, abu na cin rai na, wai yanzu Zaki ya yi aure, ya aure ƴar uwata?." Ta faɗa cikin taushin hali da fatan ace wani Zaki ne ba Saurayinta ba. " Ki ya ƙuri, abu yafi 1yr yanzu, be yi aure ba sai bayan kin fi wata 8 tukun ya yi, sabon Aure ne wanda bai jima ba. Dan Allah kar ki tashi hankalin ki kinji......" "Ya yi aure. Zaki na ya aura wata, Za...." Sai kuma sannan ta miƙe tsaye ta ce. "Na rasa shi wai !, Inaaa sam ina son sa, babu kowa acikin nan sai shi." Ta nuna zuciyar ta. Sai ta nufi in da zata kwana kafin ta shiga ta ja jakkanta, ta na kam shiga ta garƙame ƙafan. Zama ta yi jikin gadon ta sa ka sukuni da walwala. Misalin 1:21am na dare ta kunna wayarta, saƙon ne ya far shigowa a jera kuma duk na mutum ɗaya wato Monceur 💖, buɗewa tayi amma na ƙarshen kawai ta karanta. *** Daga ni mijinki Airah, ina miki so na gaskiya, dan Allah dan Allah kar ki ce za ki gujeni, ki sani ni bazan taba gudun ki ba insha Allah, ki ɗauki duk lokacin da kike so ki huta acikin familyn ki amma ki kulamin da kanki....***** Ji tai kaman ta fashe da kuka, sai kawai ta shiga contact take ta fara sanya number da ta mai wani mugun hadda, saɓo ta tura kamar haka. " A. Asad, kayi aure, ka manta da ni, Allah sarki, ya zanyi da dakon soyayyar ka da ke cin zuciyata...." ta tura tana mai jiran reply sai kawai taga ya kira ta. Take ta dauka. Zaune yake ya kasa barci tinda Sakeenat ta gama bashi labari, barcin yaƙi zuwa sai ya koma bedroom ɗin sa amma sam barcin ya guje shi, ba komai ya ke tinawa ba sai rayuwar su ta da, ya zo ace zai iya auren ta amma ina a yanzu babu aure a tsakanin su. Ganin sms ɗin ta sai ya kira, take ta fara kuka wanda ya ke ji har cikin zuciyar sa. "Ramlat is okay, Dan Allah ki shuru kinji." Ya faɗa shima kaman ya yi kukan, sai da yi mai isarta sannan ta yi shuru. sai ya dasa da ce wa. "Har yanzu wai kina sona?." "Har abada." Ta faɗa ta na share sabon hawayen idanta. "Ki na da aure ai......." "Ya sakeni wallahi ban son sa, bansan auran kowa in ba kai na." Sai kuka abinka da uwar kuka. "Innalillahi kin san ban san wanan kukan koh? Sai da safe tin da ba za ki yi shuru ba." Take ta sassauta kukan sai ya ci gaba da magana. "A kullum ban da maradi sai na ga kin dawo, na jira na jira, daga baya na fidda rai nai aure amma a kullum kina cikin rai na....." "Ka aure ni in dai da gaske har yanzu ka na so na." "Hmmmm dan ba kiji yadda ƙirji n yake bugawa ba ne, matsalan a yanzu babu aure a tsakanin mu." Ya faɗa da duk ka dauriyan sa sai ta ce "Ba aure mai ya sa?." "Saboda ina auren ƴar uwanki kuka uwa ɗaya uba ɗaya......" "Na gode." Tana faɗin haka ta kashe kiran tare da kashen wayan. A na shi side ɗin ya san haka zai faru, da shi har ita babu wanda ya rintsa har gari ya waye.. END. Tab ana abu, Ke Airah ai da auren ki kuma shi A A ya mutu a kanki sosai, haka kuma Zaki ya na ƙaunar Sakeenat amma duk da haka akwai sauran ɗanɗanon First Love AIRAH 🥰.. Ko ina Rash ya ke da tawagar sa ........ Mudai je akwai tafiya fa. Page 70. ************** ************* __________Gari na waye wa Ramlat ta koma jikin ƙofan Airah ta fara bugawa, sai ta ga ashe a buɗe ƙofar take, shiga ta yi sai ta hangeta zaune tsakiyar ɗaukin, da sassarfa ta nufe ta tana ce wa. "Why? Ba ki yi barci ba na sa ni, Airah ya kamata kisan komai ya wuce." Ta faɗa tana da fa ta, miƙewa ta yi tsaye ta ce. "Ya wuce, ban san a kuma magana, shike nan." Ta faɗa tana ƙaƙalo murmushi, duk da Ramlat ba ta yadda ba amma sai ta basar suka ci gaba da harkokin su amma sam jikin Airah a mace ya ke. ***************** ************** ___________ Bata buƙatar tambaya ta san waye Zaki, tin a kallo ɗaya ta fahimci yana cikin damuwar da ta barshi a ciki. Bed ɗin ta hau tare da daura kanta akan cinyar sa, ta na ce wa. "Faɗa min menene matsalan." Ta faɗa tana wasa da yatsun hannunsa, a rayuwar su babu ɓoye ɓoye dan haka bai ja dogon magana ya ce. "Na ka sa barci, sannan Airah ta kira ni a daren jiya, shin ni na zama azzalumi kenan tinda har na cuce ta, na kasa aurenta, sam na kasa barci saboda damuwa ta ishe ni." Murmushi Sk ta saki dan ta san dawari zan cen. Sai da ta gyara kwanciya ta yadda take kallo fuskan sa ta ce. "Babynah sam baka yaudara kowa ba, ba ka cuci ƴar uwata ba, ina so kasa wannan a ranka, a yanzu zan iya baka shafa ɗaya tak idan ka na so." "Why not, ina jinki Jaririyatah." "Ka sa mu kai da ita ku zauna kuyi magana ta fahimta, insha Allah itama za ta fahimta." "A'a bazan iya kallon cikin idanun ta ba......" "Ban sanka da tsoro ba Zaki, be a man nan." Ta faɗa da sigar wasa dan sai da ya yi murmushi, sai ta kuma ce wa. "Idan kuma ba ta yadda ba kasan mai ya kamata ka yi?." Sai ya kaɗa kai Ita kuma ta koma ta bayan shi yadda baya iya ganinta sai ga ɗaura kanta a kafaɗar sa sannan tai maganan cikin wani salo amma iyanka a baki dan ta san waye Zaki "Sai ka sake ni ka aur......." ta sauri ta rufe mata baki tare da ce wa. "Kul na ƙara jin wannan maganar, akan menene zan sa ke ki." " Baby in ba haka ba babu wata hanya ai." Da hannun sa ya sa ya zagayo da ita saitin sa sai ya ce. "Kalla cikin idanuna ki maimaita abin da kika ce." Cikin idon ta kalla babu kyaftawa, na tsawon sec amma ba ta ce komai ba sai can ta ce. "Karanta saƙon da kake gani a cikin wannan idanun nawa." Ba tare da ya ƙyafta ba ya ce. " Zallar soyayyar mijinki na ke gani." "Good, shin kaga wani tsoro a ciki." "No, sai dai na ga fargaba kaɗan." Murmushi ta yi sai ya kuma ce wa. "Ni fa mai kike iya gani a cikin idanuna." "Ban iya ganin komai sai tsabar gajiya da barci, gashi ina so na sanya ka babban aiki yanzu." "Kan ki tsaye My Queen, faɗa na cika aiki." "Yauwa so nake ka goyani muje kitchen, sai ka haɗamin abinci bayan na ƙoshi, sai na karaka gun ƙanwata dan ni ce Yaya." "Baby son girma koh, shike nan, hau." Babu musu ta hau sannan suka nufa kitchen.... *************** ************** ________ Ko bayan ya koma gida part ɗinsa ya shiga tare da rufewa, sai Fancy ce ta faɗa ma su Maa komai da ke faruwa, sunyi sunyi da ya fito ya musu ƙarin bayani amma yaƙi fitowa, gari na waye wa suka kammala komai, Dad, Maa, Fancy da M.d suka shirya sannan suka fito da sun so su tafi suka ɗai, sai A.A ya ce shima zai je. Tam kar Airah shima haka ya kwana bai yi barci. Mota biyu suka yi sannan suka nufa gidan su Fancy. ************* ************* ________ Adam ne ya kalli Spider ya ce. "Kai posting ɗin sannan ta tabbatar komai ya yi daidai, sai kai Skiddo Oga ya ce work ɗin ka ya yi sosai, a taro tawaga zuwa gobe. " Ba case, yanzu zan tura ma kowa saɓon." Faɗin Skiddo yana cin Shawarma. "Allah ya saka ma Boss, har yau na rasa ta ya zan nuna godiya ta gare shi." "Hmmm kwanda ku, nikam zan iya cewa saboda ni ya za ma RASH, dalilin iyaye na, gashi ya zama shugaban taimako, na yi imani da Allah aikin da Shuraim ya ke gaba ɗaya Nigeria babu mai kwatan sa. ina g kwanda ya fito da ainiyin sa wa muta ne dan a gyara ƙasa." "Haka ne Adam, fatan mu da mu riƙe ƙannan sa da kyau." Skiddo ya faɗa yana kiran wata number, bugu biyu aka ɗauke sai ya ce "Gobe za a dawo bakin aiki, a faɗa ma kowa." " Masha Allah gamu nan tafe." Daga haka ya katse kiran ya na duban Spider ya ce " Ka dubi yadda rayuwa ta yi da mu, mu marayu ne amma Shuraim ya mana gata sosai, na yi rantsuwa da Allah babu wanda zanga zai cuce shi na tsaya sai ƙarfina ya ƙare." "Insha Allah." Spider ya faɗa da kakkausar murya. **************** ***************** ____________ magana ce ta kai har gun Pazars, Pazar Q dan haka ya nemi da aka kira Abdullahi Ustaz da Mama Zulaikha, dan su Maa sun iso, haka Zaki da Sakeenat, sai su Ramlat da Airah, ba su jima da haɗuwa ba Mama Zulaikha suka iso. Bayan an gaisa, Pazar M ya ce " Yanzu ba wani abu ne ya tara mu anan ba face sulhu tsakanin Ramlat ko in ce Airah da Abdullahi, dan Allah ku bani a ron hankalin ku, a yanzu dai shi Abdullahi ya na son da ki koma gidan sa tinda ba sakin ki ya yi ba, dan ku ci gaba da rayuwar ku cikin aminci." Ya faɗa yana kallon Airah wacce kowa na gun ita ya ke kallo. sai ta buɗe baki a hankali ta ce. " Dan Allah za ku iya bani dama da na yi magana da Ya Umar cikin sirri." take fuskan A.A ta haɗe fiye da tsammanin dan yaji shine wanda zai aureta dan ya biya sadakin ta. "Ki tambaya mijin ki dan shi ke iko da wanna." Ta ke ta maida idon nata kansa sai ta ga ya haɗe fuska, maimakon ta tambaye sa sai tace. "Zan so na fara da kai." tana faɗin haka ta miƙe sanann ta shiga wani ɗan ɗaki daga gefan parlour, ba musu A.A ya bita, dan shima ya na so suyi magana. A zaune ya sa me ta kan kujera dan haka ya zauna a gefan ta sannan ya ce. " Airah......" "Akan meye bai faɗa min gaskiya ba?, Ashe kai kanka baka san wacce ni ba amma ka zauna da ni, harda aure na, hmmmm yanzu ka sa ke ni a lalama kawai dan bazan......." Bata ƙarasa ba ya yi saurin haɗe bakin su guri guda yana zubar da kwalla, sai da yasan ta haɗiye sauran magana tukun ya cire bakin sa sannan ya riƙe hannunta ya ce. "Airah wallahi wallahi ina sonki ina ƙaunarki, amma idan kika umarci da na sake ki zanyi, ina da kishi akan ki, ko da wasa ban yadda kifi minti uku da Umar ba." Sai ya miƙe tsaye, hannu ta sa ta riƙo hannunsa tare da kallon fuskan sa na ɗan lokaci, ba komai ne ya haska a kanta ba sai abu biyu, imagine yadda ta ya sadaukar da komai na shi a kanta, be sonta ba amma ya nemo mata lafiya, sannan rayuwar su ce ta baya ta haske a cikin kanta, rasa abinyi ya sa ta rungume sa ta na ce wa. "Ya zanyi? Ji nake Ya Umar kawai na ke so, faɗa min yadda zanyi...." "Ya isa, ki natsu da kyau kinji, ba zan yadda ni kaina na cuce ki ba, amma ki sani kina ɗauke da ciki na, ki kula bara na kira miki shi." Be bari ta ce komai ba ya fice, ji tai jikinta ya mutu, haka dai ta jaa ƙafarta ta zauna akan kujera sannan ta faɗa kanta da hannu ɗaya, ɗaya kuma ta sha cikinta. Tare ta suka shigo, bayan sun zauna, sai ta ɗago ta kalle su, Sakeenat da Zaki, wanda sun yi matukar match. "Ƴar uwa, matso kusa." Take ta matsa kusa da ita, kallon juna suke yi kaman yau suka fara haɗuwa. "Kallon kai na nake yi, hmmmm Allah na gode ma, shin za ki iya faɗa min wannan bawan Allah yana kula min da ke yadda ya kamata?." Sunyi mamakin jin abin da ta faɗa dan baka suka yi tsammani ba sam. hawaye ne suka gangaro a fuskan Sakeenat dan sai ta ji wani iri, ɗaga kai ta yi. "Faɗa min dai, idan akwai abin da ya ke miki tin yanzu na sa ni." "Babu." ta faɗa sai ta miƙe tare da fice wa da sauri ta na kuka. Ko da ƴan Parlour suka haka sai suka ce kar kowa yaje, amma zuciyar A.A har ta rayomai ce wa 'Airah ta sa Umar ya saki ƴar uwarta ne'. ________ sun dau lokacin sai ya kalle ta ya ce. " Bayan lokaci mai tsayi kin bayyana, Alhamdulillah, Ramlat ki ya femin wallahi ban yaudare ki...." "Kar ka damu Ya Umar, wallahi ya wuce, ina ji a raina haka Allah ya so, ba mu isa mu sauya ƙaddan Allah ba, ina so ka rike ƙanwata da kyau kaji." "Hmmm insha Allah, kin ya femin kenan?." "Ba komai, ya kamata na ci girma akan ka." " Ta ce ita ce babba ke ma haka to waye ni kam." "Haka ko a ido ai ansan ni ce. Ya Umar." "Na'am ka najin wani abu a ranka ga ne da ni?." Sai da sauka a in da ya ke sannan ya matsa kusa da ita amma akwai ta zara a tsakanin su ya ce. " Eh, na kasa fassara yanayin." "Nima haka ne amma mu sa a ranmu, ƴan uwanta ka ce kawai, harga Allah na haƙura domin a yanzu Doctor ke faɗamin ina da juna biyu, rabo kenan mu ƙaddara rabo ne duk ya kawo haka." "Insha Allah........" Kafin ya kuma magana sai ga A.A dan ya kasa haƙuri, sannan ya ji hiran su na ƙarshe. yana shigowa ya kalla Umar ya ce. "Ɗan Uwan ka ta yani neman yafiyarta kaji." Murmushi mai ciwo ya yi dan harga Allah sai ya ji kaman kishi ya ke yi amma ya danne komai ya ce. "Kar ka damu, ƙanwata mai yawan yafiya ce, ta yafe ma amma kamin alƙawarin kula da ita kaji." "Insha Allah, Zan kula da ita." Rungume juna suka yi, Zaki ya bar ɗakin cikin ɗan ɗauriya, A.A ya kalla Airah ya ce. "Airah ki....." "Monceur dai." Ta faɗa ta na murmushi, sai ya riƙe hannunta sanann ta kuma ce wa. "Da gaske yanzu anan akwai baby." Ta nuna cikin ta sai ya ce. "Eh, za ki bini muje gidan mu." Sai ta ɗaga mai kai. Tare suka fita suka tadda kowa yadda suke. " Fatan kun sulhunta kan ku." Abbuu ya faɗa sai Airah ta ɗaga masu kai. Komai murna ya shiga yi don ba son ace an yi saki. A gidan suka wuni sai gurin yamma suka wuce dan sai da suka je gidan Maman Rabi, suma aka basu labari, harda kuka Maman Rabi tayi sannan suka rabu nan ma A.A ya ba su kuɗi sosai. END. Page 71. **************** ************** _________ Baban labarin da ke trending a yau shine : Rash ya dawo, da sabon salo dan ya bayya kuma ya umarci duk ɗan Nigeria mai ƙofari da ya turo saƙo a wata number nan take za'a bi mai haƙƙi.. kowa labaran ya ke duba wa aka waya. Beauty da itama ke zaune a gefan Beasty ta ce. "Beasty yanzu wai duk kisan nan ashe Rash taimakon ƙasa ya ke. amma idan jami'ai suka kama shi fa? Kin san halin ƙasar nan." "Hmmm ai yanzu asirin shuwagan nin mu ya gama tonuwa kodan haka za su ƙulla mai sharri sosai." "Allah dai ya biya shi, amma yana cikin matsala tin da naji ance anƙaro jami'ai akan case ɗin, kuma President ya zauna da Governor's akan haka." Kafin Bauty ta ce wani abu sai Kandy ta shigo dan ita yanzu ta dawo daga gurin aiki. "Sannu kin shawo hanya fa." "Kedai bari Beauty, kin san yau mun sha wiya kuwa, rahota aka ce mu nemo akan Rash, yanzu haka zan kammala abin yi ne, na zauna dan duba wasu abu." "Wai sannunki, ashe yanzu Rash mutumin kirki ne? Imagine ashe taimakon mu ya ke yi." "Kedai bari Beasty, sai ma kinga channel ɗin mu yau, rahoto ne kowa da na shi." "Ina Zubee ta kawo miki drink ki ɗan sha. Zubee, Zubee." Sai ga Zubee ta fito da sauri. "Aunty Beasty ga ni." "Kawo ma Kandy abu mai sanyi." Take ta nufi kitchen sannan ta kawo mata pop cola da glass cup, sai ta amsa ta na cewa. " Ya school fatan karatun ba bu wiya." Sai Zubee ta zauna ta na ce wa. "Alhamdulillah gaskiya, makaranta ya yi, sai dai Aunties akwai dokiki next week za mu yi matriculation." " Dan Allah ki maida hankali, su kansu Uncle's ɗinki za su yi alfahari da haka." "Insha Allah Aunty Beauty." "Idan kuma akwai assignment da baki ga ne ba ki tun tuɓe ni." "An gama Aunty Beasty." ************* ************ Bayan sati ɗaya _______ a yau za ta koma school, shirya wa ta yi dan karta ɓata ma Fancy lokaci, tana gama shiri ta kalla A.A da ke bin ta da kallon ƙauna, yau ba zai fita da wuri ba dan haka yana kwance abin shi. "Monceur zan ta fi." Ta faɗa ta na ɗaura niƙaf, sai ya ce. "Please take care kinji." Ɗaga kai ta yi sannan ta fice tana kashe mai globe dan barci ya ke ji sosai. Bayan dawowanta wata sabuwar soyayya suke mai tsafta da kula da juna. Tana saukowa ta tadda Maa ta shirin shiga kitchen, gaisheta ta yi ta amsa cikin kulawa sannan Airah ta ce. " Maa ai Fatima ta kammala break fast." "Masha Allah, Allah ya muku albarka." 'Ameen' sai Maa ta koma ɗaki, zama ta yi dan jiran Fancy. * "Baby 8:00am zan shiga lecture fa, kuma Airah na jira na." Ta faɗa kaman tai kuka sai ya sake hannuta sannan ya ce. "Ni ma ai 8:00am ina da class, kawai kallon kyakkyawar fuskar ki na ke yi." "Baby please." "Okh kiss me." Ba jira ta mai peck a kumatu sannan ta fice, shi kuma ya kalla agogo 7:38am, kuma text zai ma wasu, cikin sauri ya ɗau car key ya fito, motan su Fancy na fita shima ya bi bayan su. _____ ko bayan da ya farka, wanka ya yi, sannan ya yi breakfast ɗin da ta aje mai, sai 10am ya bar gidan a lokacin har Dad ya fita Maa ce da wata Rashida mai aikin gida. ************* ************** ________ Tin a daren jiya suka iso Saudiyya, a yau kuma Abbuu ya zaga da su cikin babban burinin Saudiyya, su kansu cikin nishaɗi suke, sai bayan la'asar suka koma gida, da a hostel za su zauna Abbuu ya ce sam, tare za su zauna dan suma koma wa za suyi, dan haka suka dawo jiya, abin da ya ma su Pazars daɗi ɗaya a in da Abbuu ke koyarwa anan makaranta su Baby aka sanya su. ************** ***************** Meerah da Sakeenat ne tsaye jikin ƙofar gidan Ramlat, ba su jima ba ta buɗe suka shiga, ɗauke ta ke da Husaini da ke faman kuka, Sakeenat ta amshe shi tana jijjiga shi. "Ina Hassan hala ana sana'ar barcin koh." Meerah ta faɗa tana ajiye small Ammee kan sopa. "Aikam tin ɗazu ya ke barci, gaskiya ki faɗa min menene sirrin, naga Ammee kullum fresh ta ke ƙarawa ne, ga ta ɓulɓul." Sai suka yi dariya sannan Sakeenat ta ce. "Nima haka na tambaye ta, tubar kalla kullum sai za ma wata babban mace ta ke." Sai suka kwashe da dariya. Hira suka wuni suna sha abin su, sai suka wuce, Ramlat da duk ta shiga da muwa saboda Shuraim ya ƙi barin wanann aiki, jiya har faɗa suka yi akan haka dan haka ya fice yau da wuri, ganin kar mala'iku su tsine mata dan faɗa sukai sosi har da kuka ta yi. Wayarta ta ɗauka ta kira number sa, 3 miss call ta mai amma bai ɗauka ba kuma bai bi kiran ba. _______Sakeenat tsaki ta ɗan ja, domin ta samu ta ɗauko number Babban yaya sannan ta haɗa da na Ramlat, so ta ke ta ji wayan da za suji and duk kiran da zaiyi za ta datsa dan ta ji. Jin Earphone ɗin kunnin ta na ƙara sai ta gyara zama ta na cin popcorn abin ta. _______Ɗaukan kiran ta yi da sallama sai ya amsa. "Baby uhmm uhmmmm ni uhmmmm." _____ Jin hakan sai Sakeenat ta cire a kunnin ta aje a gefen ta. ( Hmmmm Sakeenat Allah ya shirya, ashe akwai sense Awwwnnn 💓, kunsan akwai mu da hankali wallahi.) "Ina jinki." Ya furta sai ta kuma kwantar da murya ta ce. "Ka de na so na koh?." "Ni ban ce ba......" "To me yasa kamin faɗa, ka sa ni kuka, nifa maraini ya ce." Sai ta fashe da kuka dan tina Ammee. "In kin gama kukan ki kirani." Daga haka ya katsen kiran, jitai takaici ya mata sosai, sai ta shiga contact, number da ta sanya 'My Yaya for ever' shi ta kira nan ma ba'a ɗauka ba. _______ Sakeenat ta duba kiran sai ta ga ya katse, saita abu ta yi sannan ta koma Parlour ta hau kallon T.V abinta. ________ kwanciya ta yi sai ga kiran ya shigo da farin ciki ta ɗauka ta na share hawayen ta. " Yayana ƙara na kawo maka." Ta najin sai da ya saki ɗan murmushi sannan ya ce. "Tom ƙanwata ina jinki." "Dama mijina .....mi..ji...." Sai kuka, rarrshin ta ya shiga yi sosai, har ta yi shuru, sannan ya ce. "Kimin bayani so that na baki sharawa kinji." Labarin faɗan su ta bashi tsaf ko abu ɗaya bata manta ba, bayan ya gama ji sai ya ce. "Da fari ina mai baki haƙuri a madadin shi, bara na faɗa miki abu ɗaya, kinga mijinki mutum ne mai son taimako, ki natsu ki kalla komai da idanun basira, kyanshi ki dinga taimaka masa da shawarori akan haka, ƙasa gaba ɗaya yake taimako, ko bakyaso ne?" "Ina so." "To ki dinga mai addu'a dan Allah. Shike nan ko a kwai wani complain ɗin." "Eh, dama ni ka kira shi ka ce mai karya kuma zuwa da bindiga gida, jiya na gani na tsorata sosai." "Hmmm me ya kaiki ɗakin sa, bana ha na ki shiga ba." "Eh yaya kawai dai na ɗan shiga ne." "Karki sake kinji." "Tom, Nagode a huta lafiya." Daga haka ta katse kiran. Take ya kuma kira da ɗauyan number, haka suke idan ya mata abu to ɗayan number ta ke kira ta faɗa mai komai har shawara ya ke bata sai kuma su koma dayan number. "Ina jinki." Ya faɗa bayan ya daga, ita kanta sai da ta yi mamakin sa amma ta basar ta ce. "Ka ya ƙuri." "Naji, komai sai kin kai ƙara na koh?" "Uhmmm to ai laifi ka yi ne." "Kin kyauta, fatan kin ɗau shawaran Yayanki." "Eh na ɗauka." "Na lura kina ji da Yayanki fa." "Sosai ma kuwa, baya min faɗa shi." "Ohh shike sangartaki kenan." "Yep, kuma ya ce in ka kuma ɓatamin rai za ku haɗu." Sai sukai dariya gaba ɗaya. "Kin iya drama, aiki na ke yanzu zan kira zuwa anjima." "Dan Allah Yayana na ke so ya zo yau." "Lallai ma, bakya son Mijin ki kenan." "Uhmmm ni dai ban ce ba. Bye." Ta faɗa tana kashe wayan sai ta kifa kanta akan pillow take Hassan ya farka dan haka ta miƙa ta ɗauke sa. END. Page 72. **************** **************** K.K G.R.A __________ Sai yau na ta saƙon motan ya iso, itama irin na su ne, hawa tai suka ɗan ɗana, sai suka dawo gida, itama kamar Husty ta fara attending class. "Hajiya na fi Hasty iya driving mai kyau." "Wai Hussaina ai ni na kuma hawa motan ki sai wani ikon Allah, kaɗan ya rage ranan ki ƙarasa ni." Hajiya ta kaina ta na tina ranan da suka fita. "Hajiya haka ake fama da ita, shi yasa nima ban yadda na hau motan ta, akwai ganganci." "Haba Hasty ai da ne yanzu kuwa na canza, driving na ke cikin kulawa." "Ai da kulawa shi yasa naga har motan ki ta fara ƙoƙewa and Babban yaya sai da ya miki magana." "Uhmmmm nikam Bara na shiga ciki na kwanta." Ta miƙa ta shiga part ɗin ta. "Husty manya." Hajiya ta faɗa tana mai da idonta ka T.V. ************** ************ _________ Meeting room ɗin ya dau shuru saboda jawabin da shugaban gayya ke yi wato His Excellency Haidar. "Maganar gaskiya, manyan shuwaga bannin ba su da haɗin kai, na lura da haka, ya kamata ace an nemo Rash an saka mai da halacci amma mene wai an bada dokan gani da harbi akan sa, menene shawarorin akan haka dan yanzu zan shiga meeting da jami'an tsaro." Ya kai nan ya na kallo mutanen gurin sai wani ya ɗaga hannu sannan aka bashi permission sai ya ce. "His Excellency ya kamata mubi komai a natse Rash mutum ne mai wayo da sunada, ba zai yadda a kamashi cikin sauƙin ba, kawai dai a yi yadda president ya zartar." Sai Da shima ya ce. "A ganina mu yi yadda ka ce Sir, fatan sa'a." ************ ************ _______ " Sir a yau kawai mun samu saƙo sama da dubu 1, Nigeria sai a hankali." Adam ya faɗa yana kallon saƙon nin kowa da na sa matsalan. "Mutum 20 a kullum ya isa, ki tashi ku koma gida dare na yi, nima yanzu zan wuce." A tare suka fito sannan suka hau mota suka bar wannan gidan da yanzu ya sha gyara fiye da daa. ________A haraban gidan ya tadda Aliyu da Zaki, bayan ya isa in da suke zaune shima ya zauna, ba su ɗau lokaci ba suka bar hiran tare da shigewa gidajen su. Da sallama ya shiga part ɗin sa, ganin ba kowa a Parlour ya zauna, bai jima ba sai ga ta ta fito cikin dogon hijab, kusa da shi ta iso sannan ta ce. "Rash ne ko Yayana?. " Sai da ya yi murmushi sannan ya ce. "Rash na can, yanzu yayan ki ne, Shuraim." Sai ta saki murmushi mai sanyi tana zama daga gefan sa. "Ina kewanki, ina yaran su ke?." "Sun yi barci ti ni ai." "Kifayaty ina son ki sosai da sosai." "Nagode Yayana, nima ina son ka." "Kin biya da tikwicin yara maza har biyu, kai Alhamdulillah kullum na tina wai ni ne mai yara sai naji wani sanyi na ratsani." "Ba komai, fatan ba ka jin yunwa dan yau na ce kar a ko." "Why?." Ya faɗa ya na kallon fuskanta mai wani sheƙi. "Kawai dai, mu kwana da yunwa." "A'a wallahi sam, ni a ƙoshe na ke muje kitchen ɗin." Kafin ta fara musu ya ɗauketa suka nufa kitchen ɗin. ________ Da Meerah har Small Ammee sun yi barci, gyara musu kwanciyar ya yi, sannan ya ɗauka system ya hau ɗan dube dube cikin dare, a yanzu ya samu sauƙin sosai dan wasu ayyukan Rash ke aikatawa. _______ Neman ta ya shiga yi bayan ya fito wanka amma bai ganta ba, ko ina ya duba amma ba ta babu labarin ta, harya fara tinanin ko dai ta fita ne, sai ga ta ta fito a bayan labule, haɗe rai ya yi dan yasha ne manta sai ta saki murmushi ta ce "Sorry Baby wasa ƴar ɓuya na ke so muyi." Kwafa ya yi ya koma room ɗin sa, sai ta bi bayan shi, tana shiga ko ya ɗamƙota, kunninta ya ɗan murɗa hatta saki ɗan ƙara. "Auuchhh." "Ban san kalan wasan nan." "To ni na, uhmmm shike nan, ba zan kuma yi da kai ba." Ta faɗa ta na ruba baki, ya na sakin ta sai ta fice daga ɗakin, shareta ya yi ya gama shirya barci sannan ya dawo Parlour, T.V ya kunna dan a ƙoshe yake, ko da yana jin yunwa ba zai ci ba sai ta rarrashe shi, ita kuma sai an ce ta ke yin abu, ko haƙuri wani lokaci sai ya ce tukun ake bashi. Tana kallon sa ta window yadda ya ke shashshan ƙamshi, dariya ma ya ba ta, dan haka ta miƙa da sauri kaman wacce aka kira, ba tatsa a Parlour ba ta nufi kitchen, dama kaman ta san haka ta ƙi yin girki so ta ke ta musu indomie ganin haka ta dafa guda ɗaya shafshaf, sannan ta soya egg, sai kaman ƙamshi abincin ke yi, fita Parlourn ta yi ta zauna a kujera da ke gefe guda ta fara ci a natse, saboda neman rigima ta miƙa ta ɗauki remote sannan ta mai da channel ɗin Zee world 'Barr Anu' shi ake yi, ƙara volume ta yi, shikam bai ce ko ƙala ba, ta ci gaba da cin indomie ta na kallo, guri ko da ba abin dariya bane sai ta yi. Zaki ya cika ya yi fam, sai ya miƙe tsaye, waje ya fita, take hutan nepan ta ɗauke, shuru ta yi duhu ga shi wayarta na ɗakin bincike, kuma ba ta ƙaunar duhu, da wiya kaga rauninta sai kun mungun sabo, rauninta ɗaya duhu sam ba ta juran zama a ciki. ______ bayan ya cire hutan gidan sai ya koma ciki amma ta ƙofan kitchen ya shiga, hangen ta ya yi zaune a in da ya barta ta na kiran sunan sa da cewa. "My husband ka na ina, an ɗauke huta wayana ya na kitchen, please ka shigo ka aramin na ka hasken." Murmushi ya saki sannan ya tawo cikin sanɗa ba tare da ta ji sound ba, amma kafin ya aikata abin da ya yi niyya sai ya ji ta ce. "Kana kusa, amma ta ina ka shigo?, ƙamshin turaren na gab da n...." Sai wai, wato mai gadi ya fito ya gyara hutan, juyowa tai ta ganshi tsaye sai ta marairaice fuska ta ce. "Tsora ta ni za ka yi da koh." "Mun ɓata, ba ruwa da ke." "Shike nan, ruwan juna da juna." Sai ya matso tare da ɗago fuskan ta ta kalleshi, ƙyafa idanu ta shiga yi kaman ƴar baby, ya ce. "Yaushe za ki girma? Yaushe idan kika ma mijin ki abu za ki ba shi haƙuri?, Yaushe ne idan ya faɗa abu ko bai miki ba za ki yi na'am da shi?." "Ai haka nake, kaima sheda ne." "Ke wai?." "Garantee Nawan 🥰,, sanan me ya kamata na yi kuma ina yi, irin rayuwar matan zamanin daa akwai ni da biyayya." "Shut-up, ai in zance ne kinfi kowa iya tsarawa kaman mai waƙe." "Uhmmm to ni me na yi?." "Ba ki komai ba, yunwa na ke ji." "Sai dai ka ci break banyi girki ba wallahi." "Dalili?." Yafaɗa ya na sakin fuskanta sai ta ce "Yau ni kallo na sha, na manta zan yi girki ne." "Ya yi kyau, yanzu kije kimin tuwon shinkafa miyan agushi." Waro ido ta yi sai ta kalla agogo 9:23pm, marairaice fuska ta yi sai ta ce. "Dan Allah Baby na ma indo....." "Tuwo na ke so, kefa akwai biyayya na san yanzu za ki min ai, rayuwar ki na burge ni komai irin na mutanen da kike yi." Ya kai nan da sigar wasa, miƙewa ta yi ta shiga kitchen, da ido ya bita dan tafiya ta ke tana bubbuga ƙafa. Tin da ta shiga ba ta fito ba har sai da ta kammala dan ma akwai komai a ƙasa, duba wayarta ta yi har 10:41pm ta yi, ɗauko tuwon ta yi wanda cin mutum ɗaya ta yi haka miyan haka. Kallo ya ke yi sai ta ajiye mai sannan ta nufa bedroom ɗin ta amma kafin ta shiga ta ji ya ce. "Dawo ba ki kammala ba." Kaman ba zata juyo ba sai ta dawo, ta bi ta haɗe rai. "Oyaah feed me Madam." Kaman ta kurma ihu haka tai sai ta zauna ta ɗauki spoon sannan ta fara ba shi, 4spoon ya yi ya ce. "Na gode, na ƙoshi." Kallan tuwon ta yi dan ko kwata bai ci ba, kuka ta fashe da shi kaman an mata wani abu. "Baby menene?." "Gyale ni, na ma abu ka ƙi ci, kasan wahalar girki kuwa....." Sai ta ci gaba da kukan, hannu ya sa ya riƙota ya ce. "Sorry wasa na ke miki ban na ci, jeki wanka." Miƙewa ta yi ta wuce, shikuma ya ci gaba da kallon sa dan ya ƙoshi ɗin. END Page 73. ******************** ***************** BAYAN SHEKARA HUDU. _____________ Lokaci ya jaa, rayuwa ta sauya sosai, abubuwan masu daɗi da akasin haka sun faru. bara mu dubi zuwa kowani ɓangaren dan ganin wani sauyi aka samu ko akasin sa. ***** Milinium City, Rhyneo estate ******* _______ Ma sha Allah tin da ga waje na fara ganin sauyi ba na wasa ba, ko da na shiga cikin gidan haka nan ma, main Parlour na shiga, cikin Sa'a na datta kusan kowa na gidan, harda ƴam mata uku wanda sai da nayi da gaske na ga ne su, Baby, Karis, Butter, sun ƙara girma ma sha Allah kyau da cikin halitta duk ta gama bayya a jikin su, Pazars na gani wanda duk girma ya ƙara kama su sosai, ƴar yarin ya na ga kyakykywa ta fito d gudu daga wani ɗaki, ta na riƙe da bindiga na wasa, Parlour ta iso ta ce. "Aunty kin ga twins?, Yau sai na harbi Hussain." Sai da suka yi dariya dan yadda ta yi maganan cikin hausar ta, Aunty da itama ta ɗan sauya ta kalla small Ammee ta ce. "Du ba su dai, ba kiga Aunty's ɗin ki ba ne, gaishe su." "Tom, ina kwana, ina kwana, ina kwana." Ta gaida su Baby dan ba ta san su ba, fiiii ta gudu ta bar gun. "Ina ga wata Police ɗin za mu yi." Pazars Q ya faɗa yana murmushi dan sun shan drama, sai Hajiya ta ce. "Ku shiga ku huta, zuwa anjima za suka duk sun iso." Suka amsa sannan suka shiga part ɗin su wanda sukai kewan sa sosai, shekara uku ba wasa ba, ko gida ba su waiwaya ba sai yau. ***** Air Force Base***** __________ Idanuna ne suka sauka a kan wacce har na mance da ita wato Hafsat, riƙe ta ke da mopar ta na mopping, wayarta da ke ringing ta ɗauka ganin number tsohon mijinta ya sa ta ɗauka, bayan sun gaisa ya ce. "Hafsatu yanzu na dawo da ga Kano, kuma Alhamdulillah ta ke su Yaya Bashir suka ɗaura mana aure." Kukan murna ta shiga yi, sai ta katse kiran, ta ma rasa ina za ta sanya kanta dan murna, tun bayan samun lafiyarta ta dawo gida, sai dai ba ta samu Maa da Dad ba duk sun koma ga Allah, cikin ikon Allah su Fatima suka tarbe ta cikin kula, haka suka fara sabuwar rayuwa duk da ta na cikin wani hali, dan ita ma Halima ta rasu, dan ciwo yaƙi ci yaƙi cinye wa. da sauri ta ake ta nufi part ɗin Fancy, knowing ta yi sai ta ji muryan Airah. "Yes Coming." ta shiga da murnan ta ɗan a yanzu sune ƴan uwanta, sai dan gin Dad wan suke garin kano, kuma can ta tura Muktar. Ganin yadda ta shigo ya sa Airah da Fancy kallonta sai Fancy ta ce "Aunty Hafsat lafiya?." "Lafiya har yanzu ba ku gama shirya wa ba?." "Mun gama, yanzu za mu wuce, amma faɗi abin da ke bakin ki." Airah ta faɗa suna mai da hankalin su gareta. "Yanzu Muktar ya kira ni, wai an ɗaura daga zuwa tambaya." "Kai ma sha Allah, gaskiya na ji daɗin wannan albishir ɗin." "Na gode Ummu-Affan (Fancy 😳)" "Amarya, Amarya, Allah ya bada zaman lafiya, bara muyi sauri mu dawo dan akwai meeting akan shagali bikin nan." "Hmmm Ummu-Arif kenan, to sai kun dawo." Sai ta bar ɗakin, Fancy ce ta kalla Arif da ke shan barci ta ce. "Ummu-Arif ɗauke shi muje, kinga Affan na barci a mota, badan su Butter na a nan zan barta wallahi." Daga haka suka fita zuwa coumound, motan Airah suka hau, suka ɗau hanya, Arif Fancy ta riƙe wanda ke kama da A.A, da fari mace ta haifa sai ta koma ga Allah, ita ma a lokacin ya haifa Affan, sai bayan dan lokaci ta kuma haifan twins, mace da namiji, Arif da Anam, still bayan wata biyu macen ta rasu, yanzu dai Arif shekaran shi ɗaya da rabi, shi kuma Affan Shekara 3......... ***** K.K GRA.****** _________ Motan Husty ce akwai mai dan haka nan suka shiga, suka ɗauki hanya zuwa gida, su biyu a gaba Hasty da Husty sai bayan wanda yara biyar na gani ɗaya na barci jariri yaron Hasty Ameer, kafin shi, a rana ɗaya suka haifi twins, Hasty mata, Husty kuma maza, su ma shekaran su uku, sai kuma Hasty ta kuma haifan na miji wanda watan shi hudu da kwana biyu, su ma Hajiyar su ta rasu bayan haihuwan Ameer da sati biyu, sun sha kuka fiye da zato mutum, hatta Meerah sun fita shiga yaya ni a bayyane amma dai kowa ya san Uwa Uwace. _________ misalin 1pm suka isa babban gidan na su, cikin murna aka tare be su, zaune suke a suna shan hira sai ga su Beasty, Beauty, Kandy, Beasty da Beauty sun haifa yara mata suma shekarun su 3, Beasty ƴarta mai suna Ramlat, Beauty kuma Maryam ta sanya ma ɗiyarta, Kandy ce kawai ba ta haihuba sai dai tana ɗauke da tsohon ciki wanda akai scanning twins ne. Gidan ma sha Allah ko ina yara ne ƴan dugwi dugwi sai wasa suke yi, bayan sun huta Ramlat ta shigo part ɗin, tin daga nesa na hangi irin sauyawan da ta yi, ta yi wani mugun kyau, ta yi free haka ta yi ƙiba daidai. Zama ta yi suka hira sai ta kira Small Ammee, bayan ga zo ta ce. "Kira min ƴan biyu." Da gudu ta koma haraban gidan ta kira su, da yake sune manyan a maza sun tara yara suna wasa, Ammee na zuwa suka ka mata dan dama ta sa su kuka ɗazu, duka suka mata dan su akwai cika fuska sosai, za ka za ci sun girme ta, ita kam uwar kuka sai ta fashe da kuka. A haka suka shiga main Parlour ɗin. "Small Ammee waya ta ɓa ki.?" Kandy ta faɗa sai ta ce. "Twins ne suka duke ni." "Ban hana ku taɓa ta ɓa, yayar ku ce fa." Ramlat ta faɗa tana haɗe musu fuska, da da yake Hussain shine rama kunya sai ya ce. "Mom tin da zu take dukan Hassan ni kuma ta ji ƙani, na mata gargadi (magana yaro ne) sam ba ta ji ba, shine muka mata dukka." "Innalillahi haka ka zama Hussain." Faɗin Husty. "Wannan ai baya jin, shi ne ya gado manyan ido ashe na rashin kunya ne." Kafin Momcy ta kulle ba ki ya ce. "Ni kowa ma ga na, wallahi ko." Ya yi kwafa ya na barin gurin. "Abdulraheem zo nan."ya na ji Ramlat na kiran sa ya fice. "Hmmm wallahi za ka shigo hannu ai, Hussan ma za kaje gidan Uncle Umar ka kira Maman Triple." "To sai na goyo ɗaya?." Smalla ta faɗa sai Hassan shima ya ce. "Mom ni ma na ɗauki ɗaya?." "Eh kuje." Kafin ta kuma magana har sun fice. "Allah ya shirye ku, Butter kuje ku ɗauko mata yaran, dan Sakeenat ba iya ɗaukan jarirai uku za tai ba." Su ukun suka fita, da yake unguwan akwai tsaro su Ammee har sun shiga, a tsakar gidan suka ga Sakeenat da abin turawa wanda yara jarirai uku mata ke kwance a ciki sai aka rufe saman saboda rana. Gaisheta suka yi ta amsa sannan suka jera, ita ma sai yanzu Allah ya bata, tashi ɗaya ƴan uku mata, Airah, Amrah, Afra, koya ya yi murna balle Zaki, aikam Sakeenat ta ga masoya hatta Mama Zulaikha sai da ta zo a lokacin, ta sha gata sosai, kuma har yanzu ta na samun kulawa, ƴan aiki biyu aka kai mata, tayi arba'in dan haka ta fara fita sama sama, da ƙafan da Zaki ya mata suka shiga sai ga su a gidan su Meerah, shiga suka yi nan fa gidan ya ƙara kaurewa ya hira, ga yara masu kawo complain da masu kuka, ƴan uku ne a gidan sun sha girke girke sosai. Misalin 5pm Meerah ta dawo a wata arniyar mota wanda Yusuf da Yunus suka siya mata, sai ta kyautar da nata wanda Haidar ya siya mata. Yanzu ba ta zuwa aiki sai lokaci lokaci takan leƙa, yau ma babban abu ne ya kaita. da farin ciki ta isa gurin matan gidan, ta zauna suka da sa hira, Small Ammee ta zo da gudu ta hau jikinta ta na ce wa. "Police station kika je?." "Ba sannu sai tambaya, nan naje." "Tom nima yau zan kama Hussaini za ki kulle shi koh." "Me ya miki?." "Duka na, dan na harbe shi." "Ban ha naki wasa da bindigan ruwa ba, ni wallahi na ƙosa a koma hutu, kun ishemu." Da ga nan suka sauya sabon hira, sai bayan isha'i suka watse, dan nan da sati biyu bikin three ladies, Butter lecture ne a school ɗin su, amma a Nigeria iyayen shi suke, Babu kuma wani Balarabe ne a can Saudiyya ya ke, sai Karis ita kuma a Saudiyyan suka haɗu amma a London ya ke, baban shi ɗan United States ne, mamarsa ce ƴar Nigeria. END. True love may be hard to define,but the signs to read true love can be clearly seen in every loving relationship Page 74. ************* *********** ***** RASH***** ________Tin shekarun baya ƙungiyar ta bayyana, ƙungiyar Rash wanda a duk faɗin Nigeria ake magana, a yanzu ta zama group ma fi daraja sosai, bayan dogon bincika hatta shugaban ƙasa ya ba su sanya hannu akan aikin su, aikin gaskiya da gaskiya suke yi, gaba ɗaya unguwan ba mai shiga sai mai son ganin Rash, kowa na ƙasar son ganin sa suke, amma baya bayya nuwa hatta jami'an sa wanda sunfi sama da dari uku babu wanda ake ganin fuskan sa domin wani fuske suke sanya wa mai fuskan biri, gaba ɗaya fuskan ke rufewa. Kamar kullum yau ma tawagar R.1 suka dawo shugaban ta wagan shine Damuwa R.1 (Adam), tawar Skiddo A.2, tawagar Spider S.3, sai tawagar Madaa (a cikin members ne aka zaɓe shi saboda jajirce wan shi.) Shine H.4. Sauka sukai a jerin motoci wanda a yanzu idan sun fita har binsu ake yi, yadda kasan jami'an polices haka suke, kuma cikin sanye da uniform iri ɗaya, mutane matasa da waya suna fatan ganin su a cikin wannan group ɗin na ƙasa. "Damusa, na za ci sai gobe za ku dawo." "A'a Spider, ai muna gama Meeting da Tsohon shugaban ƙasan Algeriya mukai juyo." "Okh, muma jiran Boss muke yi." Kafin ya ce wani abu sai ga Rash nan ya fito, sai da na ƙara goge idanuna sannan na kuma kallon sa, ba za ka ce Rash ɗin shekara hudun baya ba ne, saboda wannan Rash ɗin yafi wancan komai da komai, ya ƙara girma da faɗi, gemun na nasa ya cika sosai, girma da kamala sun bayyana sosai a jikin sa. ta ku ya je kamar wani namjin ɗawisu, har tsakiyar Parlour ya kawo, sannan ya zauna, Barka da fitowa suka mai sai ya ɗaga musu kai sannan ya na latsa kiran number Ramlat, bugu biyu ta ɗauka sai ya ce. "Yau dai zan cika miki burin ki." Ban ji mai ta ce ba, sai dai murmushin da ya yi sannan ya katse kiran, kallon su ya yi sai ya ce "Muje." Daga haka suka fito dukkan su, su hudu ne suka hau mota ɗaya, sai wasu moto biyu suka sa na su a tsakiya. Ba su tsaya a ko ina ba sai gidan su Shuraim. Gaba ɗaya mutanen gidan ne, dan yanzu masu huce wa ke niyyan tafiya da tini sun wuce amma Ramlat ta ce su jira Baban yaya. Ramlat ya kira sai ga su mutanen gidan sun fito dan ta ce su firfito. Sun dai ga motoci uku a tsakiyan gidan, hatta Zaki da Aliyu suna gida, Zaki ne ya kalla Sakeenat, murmushi ta sar mai, dan tintini ta shaida mai waye RASH. Mutanen ciki ne suka firfito sanye da wannan fuske ga uniform mai ɗauke da tambarin Rash. Kowa zaro idanuwa suka yi dan ganin wa'innan sai Aliyu ya matso. "Rash Members, Fatan ba wani ne ya muku abu ba." "Eh His Excellency." Ɗaya ya faɗa. Take masu tsaron gidan suka rirrige bundugu, dan ma Ramlat ta ce idan wasu motoci sun zo banda bincike an san da zuwan su shine suka bari suka shiga. "No, ko aje makaimai, me ke tafe da ku?." Kafin wani ya yi magana sai maza uku suka fito suma sanye da fuske ɗin, daga nan shima jagaba ya fito, a tsakiya ya tsaya, suna ganin shi suka san shine Shugaba domin shi ne da uniform kuma fusken sa da banbanci da na sauran. A cikin mamakin ƴan gidan ke kallon wanann tawagan, hannu Boss ya a kan mask ɗin ya cire. Take suka waro idanuwa ganin Babban yaya a tsaye. Mamaki da firgici ne ya bayya ga fuskokinsu. "Babban yaya, kai ne..... RASH." Aliyu ya faɗa cikin haɗo kalmomin da ƙyar, ɗaga kai ya yi sannan ya yi taku zuwa hudu, ya ce. "Ni ne Rash, ban so bayya muku amma Ramlat ta sanya ni, bayan yin dogon tinani na ce bara yau na bayya a gare ku." Pazars Q ne ya matso gab da Shuraim ya ce. "Shuraim ne?, To ai Shuraim baya ta fiya..." "Baba ni ne, Shuraim kuma Ni ne Rash." "Dan Allah mu shiga cikin Parlour." Ba musu kowa ya koma ciki. Rash ne ya ce. "Da fari ina neman gafaran ku, dan na ɓoye muku asalin waye ni, a gaskiya sama da shekara biyar ina wanan aiki, kafin na fara ni dama jami'i ne. Ba komai ya sa na zama Rash ba fa ce, Abokina Adam." Ya faɗa ta ke Adam ya cire fusken da ke fuskan shi, sam ba suyi mamaki ba dan sun san za su ka sance tare dama. "A lokacin baya Adam ya na rayuwa cikin kulawa iyayen shi, wata rana aka shiga cikin gidan don yin sata, ma su satan suka kashe Maman shi da Baban shi, a lokacin muna tare da Adam, ko bayan na sauke shi a mota da ya shiga, sai yaga gidan a buɗe, take hankalin sa ya tashi, tare muka shiga ciki, sai mai abin da muka tadda ba bi kyau, an musu fashi, an sace musu abubu da waya sannan an kashe mai iyaye, mun kai ƙara amma ba doka, sai ce wa suka yi, ma su irin wanann ta'asar a ƙasar nan suna da yawa. Kun san yadda na ke ji da abokina kuwa, ina son sa sosai, ko da nake jami'i na nema shuwagan nina su shiga maganar amma kowa na taɓa sai ace na bar maganan, da ga lokacin na ke da wani nufi a ƙasar nan, bayan lokacin da na tara hujjoji sosai, na yi plan aka na zama gurgu haka na ci gaba da bincin, ina fita ƙasashen waje amma ba sosai ba, ina cikin ƙasar nan, ganin idan ban yi maganin komai da kaina ba to bazan ji daɗi ba domin a binciken na ga no abubuwa da yawa akan ƙasar nan shine na ƙudirta za ma RASH." Sai ya yi shuru sannan ya da sa. " Cikin ɗan lokacin na haɗa da karu masu rai da lafiya, training sosai na koya musu, sannan da kishin ƙasar su, a cikin su ina da amintattu sune Sunusi da Mubarak." Take suma suka cire mask ɗin su, Beasty da Beauty suka waro idanu sosai. "Ina fatan ban muku laifi ba." Babu wanda ya iya magana a cikin su ma sai mamaki. Ramlat ce ta nufe sa ta rungume shi, sai kuka ya kwace mata. "Is okay, shike nan ko." "Uhm." Sai ta sake shi take sauran ladies suma suka zaga ye shi cikin murnan. Meerah da Sakeenat ne kawai ba su je ba, hatta su Momcy sun ji daɗi. Bayan sun ɗau lokaci sai Pazar R ya ce. "Ka ci gaba da taimakon ka, Allah ya biyaka, sannan wannan ga zama sirri kunji." Daga haka taro ya watse, masu tafiya gida suka huce. _______ bayan sun iso a Parlour suka yada zango, da su da yaran su, ita kuma Kandy gaba ɗaya labarin ya sa duk ta ɗan rikice, Adam ne ya ɗin ga rarrashina ta. "Ba komai ya wuce, ina jin ciwo a nan." Ta faɗa tana nuna ƙasa cikinta, kafin ya ce wani abu, sai ta fara birgima ta na jin wani azaba na ziyar tatta. Su Beasty da ke kusa suka nufeta cikin sauri. Beasty da ma aikinta ne, ta na kallon ta tace. "Na ƙuda ne, ya zo gab." "Wata takwas ne fa." Adam ya faɗa cikin ruɗani. "Ai twins ba sa yin 9 month, dole suke raba watannin, in ma 8 kowa 4 ko 10 kowa 5." Ɗakin Zubee suka shiga dan ta yi aure tini, cikin sa'a ta haihu lafiya, twins ne namiji da mace, asibiti suka je dan tantance lafiyan su, alhamdulillah komai ya zo cikin sauƙi. Zuwa safiya nan gidan ya cika dan ganin yara, Aunty ce ta yi ma Kandy wanka sannan suka roƙa ta zauna kaman yadda ta ma su Beasty. Ba yadda ta iya ta zauna. END. https://chat.whatsapp.com/LQFBwo1tifs84ZuT6X2xS9?mode=r_t By 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶 ✍️✍️ Page 75 ************ ************ __________ Rayuwa haka dai ya ke ta tafiya. babu wanda ya san waye Rash. A yau ne ake ɗaura aure su Baby ma sha Allah, hatta Abbuu ya zo, haka su Maryam, Hajara, Zainab, da itama sai yanzu Allah ya bata ciki, bayan ɓarin da ta dinga sha, amma yanzu alhamdulillah dan cikin ya shiga 7 month. Biki aka sha mai sunan biki, amare da ƴan uwanta sun sun sha kyau, amma banda Kandy dan tana gida, har kuka ta yi wai sai ta zo amma su Pazars sun hana. Biki ya yi sai godiyan Allah, hatta Hafsat wacce sati ɗaya kenan da tarewa, kuma rayuwa suke cikin jin daɗi. Amare ukun sun sha kyau na ban mamaki, kaya iri ɗaya suka sanya, doguwar riga ce irin ta larabawa fuskansu ne a waje kawai kuma riga babba ce, shigan mutum ci suka yi, dan yanzu suke gani su ce ba daidai ba, sun haddace hadisai masu yawa, sun karantu iya karatu. Misalin 4 na yamma aka kwashe amare dan duk ba bu mai zama a ƙasar. Gida sai ma sha Allah can na hangi Ramlat da Baban yaya sun haɗu iya haɗuwa, taku suke kaman basa tafiya, twins ne ke gyefan su sai suka bada wani style na daban, haka su Aliyu, sun sha kyau sosai dan kowa anko suka yi da familyn sa. Duka duka anan alƙalamin rubuta na zai tsaya ✍️, ina fatan yadda na ɗauka zai ƙayatar da faɗakar sosai, ina miƙa godiya mai yawa ga wanann ƙungiyar na wa J.A.W, da Uwar ɗakin mu wato Maman Ihsan. ALHAMDULILLAH. 𝙍𝘼𝙎𝙃 Ɓ𝙊𝙔𝘼𝙔𝙔𝙀𝙉 𝙈𝘼𝙎𝙃𝙀Ƙ𝙄 Daga ta ku har kullum PRETTY SK ce ✍️✍️✍️ Godiya ga dukkanin yabo sun tabbata ga ubangiji talikai mamallakin sammai da Kasai Allah . tsira da amincin Allah su Kara tabbata ga fiyayen halita annabi Muhammad (s. a. w) *godiya mara iyaka* GA dumbin mabiya litattafaina a Duk inda kuke cikin kasar Allah. ina matukar alfahari daku ina kaunarku kmr yadda kuke kaunata. “I will succeed. Not immediately. But definitely.” in shaa Allah. ✽‌»‌≿━༺🌹﷽🌹༻━≾»‌✽ Anas b. Malik (R.A) reported that Messenger of Allah ﷺ thus told him: *"When a non-believer does good he is made to taste Its reward in this world. And so far as the believer is concerned, Allah stores (the reward) of his virtues for the Hereafter & provides him sustenance in accordance with his obedience to Him."* حَدَّثَنَا عَاصِمُ بْنُ النَّضْرِ التَّيْمِيُّ، حَدَّثَنَا مُعْتَمِرٌ، قَالَ سَمِعْتُ أَبِي، حَدَّثَنَا قَتَادَةُ، عَنْ أَنَسِ بْنِ مَالِكٍ، أَنَّهُ حَدَّثَ عَنْ رَسُولِ اللَّهِ ﷺ *"إِنَّ الْكَافِرَ إِذَا عَمِلَ حَسَنَةً أُطْعِمَ بِهَا طُعْمَةً مِنَ الدُّنْيَا وَأَمَّا الْمُؤْمِنُ فَإِنَّ اللَّهَ يَدَّخِرُ لَهُ حَسَنَاتِهِ فِي الآخِرَةِ وَيُعْقِبُهُ رِزْقًا فِي الدُّنْيَا عَلَى طَاعَتِهِ* " . References: Sahih Muslim 2808 � ?cX僆茀$桝�欔凸W鸜竊甛厘预�,d衺n+NUm.}�櫏 葄忾g渽展家腅魖题�洄┉�9K 咕旱鹁粧穽墚Z� �驼xx�19L揣7s@熮e3i `{譜kル 𝕻𝖗𝖊𝖙𝖙𝖞 𝕾𝕶𝙍𝘼𝙎𝙃 Ɓ𝙊𝙔𝘼𝙔𝙔𝙀𝙉 𝙈𝘼𝙎𝙃𝙀Ƙ𝙄 Sakeenat Abdullahi. Oum marleekha 😍🥱🥱😅.