*NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu Nazari da aikin da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta_ ____________________________________ _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kud'i ne ga mai bukatar karanta littafin zai tura #400 kacal ta wannan accont d'in.......0542382124......Binta Umar Gtbank.....Idan kuma katin waya zaka tura to sai ka tuntu'beni ta wannan numbars din nawa zan fad'i yanda zaka/ki biya kudin......08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar karanta wannan littafi to zaku tura katin airtal ko orange na dala dari a wannan numbars......90899076 _88137740.....Dala d'ari itace a madadin d'ari uku kud'in Najeria*_ Dukan Yabo da godiya sun tabbata ga Allah mad'aukakin Sarki Allah kayi dad'in tsira ga Annabi Muhammad SAW Ina rokan Ubangiji akan yayi min jagora ga dukanin abunda na sanya a gabana. Allah yanda ka bani ikon fara rubuta wannan littafi lafiya Ina roko ka sanya na gama lafiya. Allah ka sanya in rubuta abunda zai amfani al'umma Allah ina rokan ka hane ni rubuta abunda zai cutar da Al'umma. ************************ _Kuna raina masoya a ko ina kuke a fad'in duniyar nan ina mi'ko gaisuwa a gareku masoya na na nesa dana kusa wanda na sani da wanda ban sani ba ni Binta ina matukar alfahari daku_ 💘💘💘💘💘💘💘 *A rashin sani!* Wannan littafin mallakina ne kuma 'Kirkirarran labari ne banyi don wani ko wata ba duk wanda yaga yayi dai-dai da yanayi na labarinsa to a rashin sani ne. *Gargadi da jan kunne!* Ban yarda a juya min yanayin labari na ba ta ko wacce siga ban yarda wani ko wata ya siyar min da littafi ba duk wanda ya aikata d'aya daga cikin abunda na fad'a To Allah ya isa! zan had'ashi da Allah ya bi min hakkina! *A lura* Mu lura da lokacin ibada 'yan uwa don girman Allah idan lokacin sallah yayi 'yar uwa komai dad'in da littafi yake miki ki aje kije ki gaishe da Ubangiji sai ki cigaba, Allah kasa mu dace. *Gaskiya d'aya ce daga 'kinta sai 'bata* Idan kin san zaki biya kudin karanta wannan littafi ki futar min dashi waje to kiyi hakuri don Allah bana bukatar ki, Ni ina bukatar mutane masu amana ne Littafi mallakina ne kun biya kudin karatu ne banyar da a futar min da book ba ban yarda a turawa wani ko wata ba idan kikayi min haka to Na barki da Allah!!!! *Gare ku masu siyar min da book* Ba zan gaji da cewa Allah ya bi min hakkina ba a kanku kuma bazan daina rubutu ba a kanku idan abunda kukeyi shine dai-dai a gurunku to sai ku bada himma akwai dai ranar 'kin dillanci!!!!!!! Free Pege 1 *JIGAWA STATE* Jahar jigawa Akwai wani 'karamin gari mai zaman kasan a cikin jahar, sunan Garin *Dabi* 'karamar hukuma ce guda wacce ta tara fulani usul a cikinta, Garin bashi da yawan mutane sosai Amma Allah ya albarkace su da gona ki da abubuwan more rayuwa don duk wanda ya shiga garin sai yayi sha'awar shi saboda dad'in sa suna da wuta da ruwa sannan suna da makarantu na boko da isilamiyya da allo Gaskiya Mai wakilatar garin yana kula dasu sosai, Jama'ar dake cikin garin *Dabi* suna da wayewar kai babu laifi sai dai idan suka fito cikin gari ne suke komawa 'yan kyauye mussaman idan suka shigo garin *Kano* sai suji tamkar a saudia suke saboda tsabar murna. Yawancin jama'ar garin 'yan uwan juna ne shiyasa suke zumunci sosai da sosai sam baka ta'ba jin wata 'baraka ta fito daga cikin 'karamar hukumar saboda suna da had'in kai kuma suna aiki da Iliminsu dai-dai gwargwado. Wata 'katuwar 'kofa na kutsa kaina ciki na fara rarraba idona. Kofafin na gani sun kai ashirin da wani abu kuma ko wace 'kofa akwai mutane a cikinta can na hango wata Matashiyar budurwa ta futo daga wata 'kofa a guje! tana nema ta bugeni nayi saurin kaucewa ina binta da kallo naga ta nufi babbar kofar da zata sada ka da ainihin 'kofar gidan gabad'aya.....Kafin in dawo daga tunanin da nakeyi na hangoshi yana talle mata 'keya tare da haurinta da takalminsa irin na sojoji ita kuma sai murza ido take tana zum'bura baki. Nayi saurin 'buya bayan gatanga har suka wuce inda nake la'be sai na fito a hankali na bi bayansu. 'Kofar da yarinyar ta fito nan naga sun nufa sai na rufa musu baya domin inga 'kwal Uwar daka. Tana zaune tana gyara fitilar 'kwai irin mai kamar a ci balal d'in nan sai mita takeyi tana fad'in "Marka kinga ja'irar yarinyar nan ko sai dai ta fasa min 'kwan fitila sannan taji dad'i." Marka dake zaune a kofar d'akinta tana kad'in lagwani tace"Aifa! Ladidi kin manta halin Sayyada kenan nazo fitowa daga 'bandaki naga ta farara da gudu tana dariya sai kace wacce tayi abin arziki." "Ki rabu da ita Marka ai yau sai na zane mata jikinta wallahi ki duba ki gani 'kwan fitila ta ya kai shekara guda a jiki amma sai da tayi sanadin sa har sauran kalanzir d'ina sai da ta zubar." Marka tana kad'i tace"Kamar gaske ai ba zaki iya dukanta ba humm! sau nawa Sayyada nayi miki laifi kice zaki hukunta ki kasa Allah dai ya kyauta mutum d'aya ne yake maganin Sayyada." Tace."To ki zuba ido kisha kallo yau sai na hukunta ta kan 'barnar da tayi mi........Kafin ta 'kara maganar ta sai suka jiyo gunjin kukanta daga soro! "Wayyo na shiga ukana!! Wayyo baba Ladidi Wayyo Baba hiiiiiiii!hiiii! Wayyo Allahna baba Ladidina."!!!!!!! Ai da sauri Baba Ladidi ta mi'ke don har zaninta ma ya kusa fad'uwa tayi sauri ta gyara tace" Marka kin gani ko ta futa an zalince ta kai! jama'a mutane basu da tsoron Allah yanzu daga futar ta ko minti biyu bata yi ba har an doko t.......Maganar ta ta katse lokacin da ta hango shigowarsu yana talle mata 'keya tare da rankwashinta aka. Komawa tayi ta zauna tasha kunu! tana hararasa. Baba Marka ta washe baki tana fad'in"Maraba lale sannu da zuwa soja marmari daga nesa sannu da zuwa sannunmu zauna ga gurin xama na gyarama ka." Tafada tana shimfida masa tabarmar dake kusa da ita a jinge ne. A nutse ya cire takalmin sa ya zauna cikin nutsuwa yana gaisheta.....Baba Marka ta amsa cike da walwala da farin ciki tace"Ashe ka shigo gari shiyasa naji waccan kafirar tana kuka dama ai yanzu yanzu nake fad'in kai kad'ai ne maganinta." Ya kalli gefan da suke zaune Baba Ladidi ta tsuke fuska sam! ta'ki dariya ballanta ta sakar masa fuska saboda ya doki 'yar gidanta. Fuskar nan a had'e yace."Baba na same ku lafiya."? Tace"Yo da baka sameni lafiya ba ai ba zaka ganni a zaune da'kau! ba haka kawai daga saukar ka sai ka fara cin zali ni bana son haka wallahi." Shiru yayi yana kallonta tsawon minti sai ya girgixa kansa kawai ya mai da hankalinsa kan Baba Marka suka cigaba da hirarsu. Sayyada ta zauna kan 'kafafun Baba Ladidi tana shar'bar majina tare da kuka wiwi "Allah ya saka min Baba wai me nayiwa wannan ne ya tsaneni! kullum sai ya dakeni Allah ya isa ban yafe ba."!!! Tana kuka take wannan maganar fuskarta duk tayi jage-jage da hawaye. Ya juyo yana kallonta Tayi sa'ke_sa'ke! kan lanjararrun 'kafafun Baba ladidi wanda da 'kyar take tafiya dasu amma saboda tsabar so da sangarta ta bari Sayyada na tumurmusar su........Sarkin Zuciya da miskilanci kawai sai ya mi'ke! a fusace ya zare blet din 'kungunsa ya shiga tabka mata a jiki. Daga Sayyadar har Baba Ladidin gigicewa sukayi Baba sai kare Sayyadar take wai kar ya daketa shi kuma yana sane ya dinga labta mata blet din ta ko ina!! A guje! ta mi'ke ta nemi hanyar tsira bayan Baba Marka ta 'buya tana makyarkyata! Baba Ladidi ta saka kuka tana fad'in" Wannan rashin imani da yawa yake Wallahi tallahi Sadam! zanyi maka Allah ya isa kan kana dukan 'yar nan zan iya bar muku garin gabad'aya mu koma wani gari ina dalili umm! me yarinya tayi maka kawai zaka tsane ta babu dama ka shigo gari shikkenan hankalinmu ya tashi yau har dani ka had'a ka doka tom zamu bar muku garin *Dabi!!."* Tana gama maganarta sai ta dingisa kafafu ta shige d'akinta tana share hawaye. Sayyada ta mi'ke zata bi bayanta ya buga mata wata razananniyar tsawa"Koma ki zauna munafuka 'kazamiya kawai."! Ta koma ta zaune tare da sunkuyar da kanta 'kasa! duk rawar kanta tsoron sa takeyi mutum sai kace mala'ika mugunta a cikinsa har da ta siyarwa gashi tunda take dashi bata ta'ba ganin dariyarsa ba. Mi'kewa yayi fuskar nan a murtuke ya nufi d'akin Baba Ladidi.....Ya shiga ya tarar da ita tana had'a kaya cikin wata tsohowar akwati. 24/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu masu nazari da aiki da Iliminsu, burin 'kungiyar a ko da yaushe ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyan ta_ _____________________________________________ *_Littafin Ni da Yaya Sadam! na kud'i ne 1 _ 2 ga mai bukatar karanta littafin zai tura #400 kacal ta wannan accont d'in.......0542382124......Binta Umar Gtbank.....Idan kuma katin waya zaka tura to sai ka tuntu'beni ta wannan numbars din nawa zan fad'i yanda zaka/ki biya kudin......08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar karanta wannan littafi to zaku tura katin airtal ko orange na dala dari a wannan numbars......90899076 _88137740.....Dala d'ari itace a madadin d'ari uku kud'in Najeria_* Free pege 2 Ganin inuwar mutum a tsaye a kanta yasa ta d'ago kanta suka had'a ido sai tayi saurin mayar da kanta 'kasa ta cigaba da harhad'a kayanta. Ya lalla'ba a hankali ya shiga d'akin ya samu gefan gadon karfenta ya zauna yana me sassauta fuskarsa, yace."Baba Ladi." Banza tayi masa ta cigaba da harhad'a kayanta. Sai ya sakko daga gadon 'karfen ya gurfana gabanta tare da ri'ke hannunta yana kallonta a marairace yace."Wai me yasa yanzu kika daina sona ne."!? Da hanzari tace"Saboda kana zalintar marainiyar yarinya." Ya sassauta muryasa tare da fad'in"Wannan ba zalinci bane Baba gata ne wallahi idan kikayi sake da Sayyada a haka watarana sai ta sanya ki kuka wai me yasa kika sakar mata take abunda take so macace fa duk rintsi aure zakiyi mata amma kawai saboda sangarta kin sakarwa yarinya tana shashanci har yanzu ta'ki hankali." "Au! Abunda zakace kenan Sadam."!? cike da mamaki ta fad'i maganar. Yace." Ai gaskiya na fad'a Baba yanzu a irin wannan shashancin da yarinyar keyi cikin 'kauyen nan waye zai aureta anya ma tana zuwa makaranta kuwa."!? Baba Ladidi ranta ya 'baci da jin abunda yake cewa tace"Wato har ka manta al'kawarin dake kanka kenan har kakewa Sayyada maganar aure da wani." Ya mutsa fuskarsa yayi yace."Wane al'kawari ne a kaina? na fad'a miki tun wuri ki daina wannan maganar abunda ba zai ta'ba faruwa bane." Baba tace"Dama ai nima bance dole ya faru ba amma me yasa ka d'auki al'kwari kasan baza ka iya cikawa ba."? Yace."Kawai saboda in kwantar mata da hankali yasa na d'auki al'kawari amma ni ko a mafarki banta'ba tunanin zan auri waccan shashashar ba." Baba tace"To wannan abun kunyar baza'ayi shi dani ba a wannan garin wallahi tattara nawa zanyi in bar muku garin dama kun saba da abun kunya." Yace."Ke yanzu kan Sayyada sai ki bar mahaifarki? garin da aka haifi iyayenki kan wata 'karamar alhaki sai ki bar tushen ki."! "Idan ta kama hakane zai faru."! tafada tana kokarin rife akwatin tace" Kaga ma na had'a kayana guri guda Duk sanda Mahaifinka yazo muka tattauna kan maganar naga ya baka goyon baya sai in dauketa mu bar muku garin." Miskilin murmushi yayi ya d'an kishingid'a kan fillo yana kallonta tana surutai ta gama ta futa daga d'akin tana fad'in "Mutukar kai da mahaifinka kuka karya al'kwari kun ci amanarmu." Babu kowa a tsakar gidan don Baba Marka ta d'auki kayan kad'in ta ta nufi gidan d'anta dake cikin kofar wannan damar Sayyada ta samu sai ta fuce daga gidan gabakid'aya ta fara bin gidajan mutane tana musu 'barna da shirme duk gidan data shiga in ta dame su zasu koreta idan taji haushi kawai sai tara dutsinan wuta ta hau jifansu dashi tana zaginsu Baba Marka na zaune a soron gidan d'anta mai suna Kawu Tanko Sayyada ta shigo a guje har sai da ta take mata 'kafafu ba tare da ta juyo ba ta afka cikin gidan tana 'kwalawa Amina kira "Ke Amina kina ina! ki fito kiji."!!! Matar Kawu Tanko mai suna Iyatu tace" Ke Sayyada baki da hankali zaki shigo a guje kina ganin Baba a zaune amma kika bi takan 'kafafunta." Zum'bura baki tayi tace"Baba Iya Wallahi Baba Marka muguwa ce ita ta ri'keni wannan mugun mai ba'kar fuska ya dakeni da blet shiyasa ina sane nima na take mata kafarta." Ta karasa maganar tana wata iriyar dariya." Amina ta shigo da bokitin ruwa a kanta a guje Sayyada tayi kanta ta ru'kunkume ta tana ihu! kafin kice kwabo sai gasu a 'kasa ruwan ya rube a jikinsu sun ji'ke jagab! Sayyada ta mike tana kyalkyala dariya dankwalinta ta cire duk yawan gashinta sai da ya jike duk ya kwanta a gefan fuskarta doguwar rigar ta ta jike sai digar da ruwa take 'kananun nonowanta da suka fara fitowa suka sake tsini duk shatinsu ya fito hatta da nipples din sai da suka nuna alama duk da cewar doguwar rigar ta atamfa ce. Baba Marka ta girgiza kai tace"Wannan yarinya ban san irinta ba wallahi yanzu yanzu fa Sadam! ya daketa amma da yake jikinta na ice ne har ta wartseke tana ibilici Shashasha mara nutsuwa ai zan sanya Sadam! din ya sake zane ki tunda bakya jin magana." Amina tace"Baba da gaske kike Yaya Sadam! ne yazo."? Baba Marka tace"Kaji ni da yarinya dama ni ina karya ashe."!? Sayyada ta kyalkyale da dariya tace"Baba bakya 'karya sai dai ki fad'a ba dai-dai ba." hahahaha ta karashe maganar tana dariya. Baba Iyatu takaici ya isheta sai ta dauki takalmi ta nufe dashi tana fad'in "Don 'kaniyar ki Uwar tawa kike 'karyatawa a gabana." Sayyada ta ruga a guje han fita ta nufa tana dariyar hauka had'e da tsalle-tsalle.....Da sauri Baba Marka ta janye 'kafafunta tana fad'in"Yanzu sai tabi ta kaina ba hankali ne da it.......Kafin ta 'karasa maganar da takeyi taji bururut!burut!!! Sayyada ta sakar mata tusa a kanta a guje! tayi waje tana dariya. Baba Marka ta toshe hanci! tana yun'kurin tashi ta bar gurin saboda tsananin warin tusar....Baba Iya kuwa dariya ce ta su'buce mata tayi mai isarta tana nemawa Sayyada shiriya gurin Ubangiji. Amina a gurguje ta sanja kaya ta bi bayan Sayyada can Kofar Baba Ladi. Karo suka buga ita dashi kirjinta ya daki kirjinsa....A gigice ta kwallara 'kara ta d'ago kai tana kallonsa rintse ido tayi tana tsalle had'e da harfar da hannuwanta kamar wacce ta 'kone fad'i take "Wayyo Allah na! Wayyo 'Kirjina wayyo 'kirjina Na shiga ukuna."!!! Ya zuba mata ido yana kallo jikinta a ji'ke jagab! babu abunda bai gani ba a jikinta ga 'kirgar dangin ta nan yayi cibir dashi a tsaye yayi saurin kauda kansa daga kanta....Ita kuma bata fasa ihun da takeyi ba, Tsawa ya daka mata " Ke don ubanki yi min shiru."!! Tsit! tayi tana kallonsa da idanunta masu rikita masa lissafi Ya dauke kansa yana cizan lips dinsa na 'kasa mugun haushin yarinyar yake ji wallahi ya rasa wane irin horo zaiyi mata wanda zatayi hankali sai kaje mai sarkin aljanu aka. "Hiiiiiii!! Wayyo Kirjina zafi suke min wayyo nan d'ina wayyo Baba Ladidinaaaa!!!! Sosai ta 'bare baki tana kuka sai hawaye ne yake shatata da alama dai da gaske take 'kirjinta zafi yake. A dake! yace." Ina ne yake miki ciwo a 'kirjin naki."? Nonowanta ta nuna masa duk guda biyun. Yayi sakare yana kallonsu da mamaki a tare dashi Ina abun yake? da har dan an zunguresu zasuyi ciwo yanzu dai idan ya fahimta had'a 'kirjin da sukayi ne ya sanya take wannan kukan kamar wacce aka yanka. Cike da mugunta ya kai hannunsa kan brest din ya murd'e da 'karfi! "Wayyyo! Wayyo! Allah."!!! Sai ta zube a gurin tana wani irin jan numfashi. Ya tsugana gabanta tare da tsira mata lumsassaun idanunsa yace." Duk sanda kikayi laifi zan dinga hukunta ki da wannan tunda naga duka baya d'aukari dan uwarki! zan dinga murd'e miki nono sai kiyi kukan da hujja."! Ya mike tsaye ba tare da ya bi ta kanta ba ya nufi 'kofar su Kawu Tanko domin su gaisa yana so ya koma da wuri karo suka ci da Amina. 24/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION🖊📚* *M W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu masu Nazari da aiki da Iliminsu, burin 'kungiyar a ko da yaushe ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyansu_ _________________________ _____________ *_Littafin Ni da Yaya Sadam! na kud'i ne 1 _ 2 ga mai bukatar karanta littafin zai tura #400 kacal ta wannan accont d'in.......0542382124......Binta Umar Gtbank.....Idan kuma katin waya zaka tura to sai ka tuntu'beni ta wannan numbars din nawa zan fad'i yanda zaka/ki biya kudin......08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar karanta wannan littafi to zaku tura katin airtal ko orange na dala dari a wannan numbars......90899076 _88137740.....Dala d'ari itace a madadin d'ari uku kud'in Najeria_* Free Pege 3 Amina na hangoshi ta nutsu cikin nutsuwa take tafiya har suka had'u ta saki fuska sosai tace"Ya Sadam! ashe kazo sannu da hanya yasu Kawu da Yaya Sule dasu Muniba."? Yace."Kowa lafiyar sa lau Amina dafatan na same ku lafiya."? ''lafiya kalau wallahi."Tafad'a tana sinne kai. tsai yayi yana kallonta ya lura yarinyar na jin kunyarsa ya rasa kuma meye dalili hankalinta da nutsuwarta yana mugun burgeshi ba kamar waccan mahaukaciyar ba Sayyada. Yace."Ina fata dai kina zuwa makaranta."? Tace"Eh ina zuwa a boko ma nice nazo ta d'aya Isilamiyya kuwa sai da aka bani kyauta saboda na haddace izifi biyar da ka." A take ya saki fuskarsa sosai tamkar gonar audiga yace."Babu shakka nima ta 'bangarena dole in miki kyauta Aminatu kin burgeni gaskiya da zan koma kaduna yau amma saboda ke zan zauna inyi kwana biyu ina so in saurari karatunki idan anjima da daddare." Amina tayi murmushi tace"To shikkenan Yaya Sadam!. Yace."Bari in shiga mu gaisa da mutan gida ko." Tace."To." Ya wuce ya barta tsaye a gurin Amina bata dauke kanta daga kansa ba har sai da taga ya shige kofar su sannan ta wuce ta tafi. "Wai Sayyada wannan kukan da kikeyi na menene."!? Baba Ladi ce tsaye kan Sayyada wacce ke zaune a dokin 'kofa tana kuka harda majina. Baba tace" Wai ba magana nake miki ba kinyiwa mutane shiru wallahi Sayyada ki bar ganin ina kyaleki kan abunda kikeyi min ina tara ki ne akwai ranar da zan zane ki da bulala da kaina ai banji takaicin dukan da Sadam! yayi miki haka kawai saboda tsabar rashin ji kika fasa min 'kwan fitila shekarar abina biyu amma kinyi min sanadinsa." Baba Ladi ta dage sosai tana mata fad'a irin wanda bata ta'ba yi mata irinsa ba. Sayyada ta kwanta a kasan gurin tana kuka lokacin ne kuma Amina ta shigo. "Baba wai me akayi mata take wannan kukan."!? Amina ke tambayar Baba Ladi. Baba Ladidi na 'kokarin kad'e tabarma tace" Oho mata ai ta saba laifi idan anyi mata fad'a tazo tana kuka." "Nifa Baba ba haka bane ba za'a tsaya a ji ta bakina ba sai kawai ayi tayi min fad'a."!! Sayyada ke wannan maganar lokacin da take dafe 'kirjinta da hannunta. Baba Ladi tace" Ai sai ki fad'i dalili ba ki zauna kina kuka ba." Tace."Baba nan d'ina ne yake min ciwo."! nononta da ya murd'e take nuna mata. Baba Ladi ta aje ta barmar ta karasa inda take kwance tace"Tashi zaune ki nuna min." Sayyada ta mi'ke da kyar tana nuna mata brest din nata wanda yafi ciwo tace"Yaya Sadam! ne ya murd'e min."!! Baba Ladi ta buga salati tana tafa hannu tace"Kika ce Sadam ya murd'e miki nono kan wane dalili? ai wannan mugunta ce kowa ya sani idan mace ta fara 'kirgar dangi sunayi mata zafi idan ba so yake ya kashe ki ba kan wane dalili ma zai ta'ba miki jiki bayan ance ya aure ki ya'ki."!!! Baba Ladi ta shiga sirfa bala'i inda ta nufi kofar d'akinta inda mayafinta yake rataye a kofa ta nan nad'e shi ta d'ora aka sai kace wacce tayi gammo wai ita nan yafa mayafi tayi sai ta nufi hanyar fita tana d'ingisa 'kafa "Wannan ai kafirci wato yaje yayi mu'amula da turawa 'yan bana bakwai sun 'bud'e masa ido da iskanci shine yazo zai dinga latsa yaran mutane to kuwa zai ci ubansa."! Bayan fitar ta Amina ta Kalli Sayyada dake goge hawaye tace" Wallahi Sayyada 'karya kikeyi kice Yaya Sadam! ya ta'ba miki nono wallahi kiji tsoron Allah meye abinda zai burgeshi a jikinki mutum da yake mu'amula da 'yan gayu yaje 'kasar waje yayi karatu yayi cud'anya da turawa masu kyau da ilimi shine har zaki ce ya ta'ba miki nono ni dai ban yarda ba." "To kada Allah yasa ki yarda mana dama ai ba so nake ki yarda ba aikin banza kawai kamar yanda yake dan uwanki nima haka yake dan uwana harda zaki wani tare masa ai dake ya ta'bawa ba zakiji dad'i ba ke ko kishina ma bakya yi wallahi nasan irin zaman da zanyi dake." Amina tace"Ai halinki na sani na sharri da shirya magana sai kiyi ta rantsewa kan abunda ba'ayi ba wallahi Sayyada kiyi hankali ki daina abunda kikeyi." Sayyada haushi ya sanya ta soma zagin Amina kafin kice kwabo sun kaure da fad'a har da kokawa Sayyada tayiwa Amina lilis ta zaneta tace"Idan kinje kice yazo ya rama miki shi wanda kike tarewa fad'an." Amina na kuka ta nufi 'kofar su....Ita kuwa Sayyada sai ta kama hanya ta fice daga cikin kofar gabad'aya gidajan amare ta fara bi tana musu wanke wanke da shara yayi al'kawarin ba zata dawo gidan ba sai dare sai ta tabbatar ya bar garin sannan zata dawo. Baba Ladidi ta nufi kofar su Kawu Tanko saboda tayi ya'kinin yana can aikuwa samunsa tayi zaune kusa da Baba iyatu da Marka suna hira ga 'kwaryar fura a gabansa yana sha. Tana shiga ta sauke mayafin dake saman kanta ta rataye kan igiya.....Tace."Kai ja'iri gurinka nazo yanzu zan tona maka asiri ehe! wato dama abunda kaje ka karanto kenan iskanci."! Sadam! Ya aje ludayin dake hannunsa ya had'e fuskarsa sosai yasan hargitsi irin na Baba Ladidi shiyasa yaci mur yana kallonta. Ita kuma ta kalli Marka tana numfarfashi tace"Yanzu Marka dai-dai kenan abunda Sadam! yayi iye!? Haka kawai saboda son zuciya yarinya na irgar dangi ya kama mata nono ya murd'e wannan ai iskanci ne da yahudanci yarinya kamar Sayyada me ta sani."!? Marka da Iya suka sanya salati suna tafa hannu." Sai su mayar da hankalinsu kansa......Dake mutum ne mai mutukar 'kwarjini da iya waskewa ko alama basu fuskanci razana a tare dashi ba sai ma wani kwarjini da yayi musu wanda suke ganin kamar ba zai iya aikata wannan d'an yan aikin ba. Baba Marka tace"Haba Ladi! Wai kin manta halin Sayyada ne? hummm! gaskiya banji dadin jin wannan maganar ba haba jama'a! ai a fad'i abunda zai faru amma wannan dai karya ce Har guda nawa Sayyadar take haba jama'a!!!! Baba Iya tace"To nima dai abinda na gani kenan Sadam! ba zaiyi wannan al'amarin ba. Yace."Baba Marka ku kyalesu don Allah ni nasan saboda me yasa ta fad'i haka saboda d'azu ta tisa ni a gaba wai dole sai na auri sayyadar nace bana so a kai kasuwa shine suka 'bullo da wannan zancan to ni me zanyi da wannan mahaukaciyar yarinyar 'kazamiya." Baba Ladi ta maka masa da'kuwa tana fad'in"Ubanka ni ce nake maka 'karya ko? Wad'annan kafiran idanun naka menene ba za ka iya ba Ai ni na yarda da abinda Sayyada ta fad'a su dai da kayi musu kwarjini sai su 'karata maganar auran Sayyada kuma ni na yanke hukunci." Murmushi yayi kawai ya sadda kai 'kasa yana me cigaba da 'kur'bar furar sa. Baba Marka ta kalleshi a nutse tace"Haba Sadam! ashe kana so ka bamu kunya kenan."!? Ya kalleta a nutse yace."Wace iriyar kunya kuma."? Tace."Naji kana maganar kai ba zaka auri Sayyada ba karka manta da cewar Kaine kayiwa mahaifiyarta al'kawari zaka aureta kafin rasuwarta kayi 'kokari ka cika wannan al'kawari." Yace."Baba lokacin da nayi alkawarin zan auri yarinyar Baba Indo na cikin halin ciwo lokacin inaso taji sau'ki ta dawo cikinmu mu cigaba da rayuwa kuma a lokacin da 'kuruciya a tare dani amma ni har ga Allah ba wai na amince bane zan auri yarinyar ina me baku hakuri kuma ina mata fatan kan Allah ya bata miji nagari wanda ya fini nutsuwa da komai da komai. Baba Ladidi ta saka kuka tana fad'in"Wallahi kai ba d'an halak bane Sadam! yanzu meye laifin Sayyada umm? yarinya san kowa 'kin wanda ya rasa yarinyar ma tafi 'karfin ka matar manyar mutane ce amma saboda muna so mu cika al'kawari muna ta binka kana mana wulakanci kar Allah yasa ka aure ta d'in." Ta dauki mayafinta dake rataye a kan igiya ta nufi hanyar fita tana share hawaye. Amina ce ta shigo tana kuka. Baba Marka tace"Ke kuma meye kike kuka. Ba tace komai ba ta shige daki tana share hawaye duk sanda zasuyi fad'a da Sayyada ita take cin galaba akanta ta rasa menene dalili. Baba Marka ta dinga rarrashin sa kan ya daure ya auri Sayyada kamar yanda yayi alkawari a can baya....Domin ya kwantar mata da hankali yace."Zai yi tunani kan al'amarin. 24/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *_Littafin Ni da Yaya Sadam! na kud'i ne 1 _ 2 ga mai bukatar karanta littafin zai tura #400 kacal ta wannan accont d'in.......0542382124......Binta Umar Gtbank.....Idan kuma katin waya zaka tura to sai ka tuntu'beni ta wannan numbars din nawa zan fad'i yanda zaka/ki biya kudin......08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar karanta wannan littafi to zaku tura katin airtal ko orange na dala dari a wannan numbars......90899076 _88137740.....Dala d'ari itace a madadin d'ari uku kud'in Najeria_* Free pege 4 Sayyada tunda ta fita daga gidan bata dawo ba sai gab da magariba tazo shigowa sukayi kici'bus dashi ya fito daure da alwala da nufi zuwa massalaci ya kalleta ta kalleshi babu tsoro a tare da ita ta zabga masa tsaki tare da fad'in "Dan iska kawai." Sadam! ya bita da wani irin kallo na mamaki yanzu shi Sayyada ta kira da d'an iska? Zuciyarsa tace masa ka ta'ba mata nono dole kira ka da wannan sunan.....Tabbas hakane daya sashen na zuciyarsa ya fad'a masa haka. Girgiza kansa kurrum yayi yayi gaba yana tunani kan al'amarin sam bai ta'ba jikin yarinyar da wata manufa kawai sai dan hukunci yanda ya fahimta yarinyar da kakarta sunyi masa wata fassara ta daban tabbas zai nunawa yarinyar shi d'in 'dan iska ne kamar yanda ta kira shi zai dinga murd'e nono da take ta'kama dashi. Da 'kyar Baba Ladidi ta tirsasata tayi sallahr magariba sannan ta d'auki kayan tallanta ta fita can bakin wata katuwar bishiyar darbejiya ta nufa ta aje farantin gyadar marau da tibis Baba Ladi ce take soyawa duk daran duniya Sayyada na dauka ta fita dashi cikin ikon Allah sai kiga anyi cini dari dari biyu a cewar Baba Ladi ta siyi kalanzir da sukari na koko sana'a ko yaya take dad'i gare ta. Tare da Kawu Tanko suka fito daga massalacin suna tafe suna hirar yaushe gamo Kawu Tanko na tambayar d'an uwansa Sadam! yace."Yayi tafiya zuwa Abuja wata uku zaiyi ya dawo insha Allah......Sai da suka zo dab da bishiyar da Sayyada take ya hangota matasan maza 'yan bana bakwai sun kewaye ta sai wasan banza suke d'aya har yana cire mata d'an kwali. Gabansa ya fad'i sosai! sai yaja ya tsaya yana kallon Kawu Fuskarsa a d'aure yace."Kawu waccan yarinyar ba Sayyada bace."? Kawu Tanko ya kalli inda yake nuna masa ya hango Sayya tsakiyar maza. Yace."Itace ai nan ne gurin da take zama siyar da gyada Baba ke kasa mata tallah da daddare." Sadam! Yaji kamar ya gaura masa mari! wannan ai cin amana ne yarinya marainiya suka zuba ido suna gani ta dauki hanyar lalacewa. Yace."Haba Kawu! Haba duba fa ka gani Kawu kuna raye wannan al'amari yake faruwa! kar fa ka manta da cewar yarinyar nan amana ce a gurinmu Baba Indo bata cancanci wannan abu ba." Kawu Tanko jikinsa yayi Sanyi kalau yace."Sadam! wallahi tallahi nayi dukanin iya bakin kokarina kan hana faruwar wannan al'amari Baba ta'ki fahimta akwai ranar dana zubar da gyadar a cikin kwata a ranar Baba sai da ta kusa tsine min kuma tafi sati bata amsa gaisuwa ta wallahi shiyasa nake jin tsoron shiga lamarin saboda gudun bakin uwa amma dukaninmu munyi iya bakin kokarinmu kan al'amarin." Girgiza kai kurrum yayi ya nufi bakin bishiyar ba tare da yace komai ba. Kawu Tanko ya bishi da kallo ya riga yasan halin Sadam! da ba'kar zuciya da gudun magana da zai dauki shawara sai yace kawai ya amince a daura musu aure shine zai kawo karshen matsalar. Matasan samarin na ganinsa ya doso gurin sai suka watse kowa yayi nasa guri ita kuma tana fad'in" Kai Talle mai abin dariya kar'bi canjin ka wallahi ko kuma in had'a dashi cikin lissafina." Talle yace."Kije na bar miki budurwata ai kin fi karfin komai a gurina." Kyalkyalewa tayi da dariya tana gyara daurin dankwalinta tace"Talle kenan waye ya fad'a maka ni zan auri d'an 'kauye humm! mijina d'an birni ne kyakkyawa Soja mai aj.........Kafin ta 'karisa tagan shi a tsaye a kanta. Mi'kewa tayi da sauri! tana mutsika ido ta fara zumbura baki jelar d'ankwalinta ta kamo tasa a baki tana taunawa tamkar wata shshasha! nan kuwa tsabar iskanci ne yayi mata yawa. Sadam! Ya kalli talle dake tsaye tirmin danya shi ya'ki tafiya yana sanye da wani yadi fari yayi masifar daud'a duk yayi jirwaye mussamam hamtar sa da bakin aljihunsa sai wata shegiyar hula da ya kwafa a kansa sai kace kwano sa wani tabarau wanda yayi masa yawa.Shi nan bai yarda ba yayi gayu. Sadam! mutum ne mai 'kyamkyami sosai shiyasa kallo guda yayi wa Talle da yaga bakinsa dagaje-dagaje yayi saurin kauda kansa yana ya mutsa fuska......Yace."Kai wuce ka bawa mutane guri dallah."! Talle ya ya hau ya'ke yana sosa 'keya yace."Ya asalin na wuce muna hira da masoyiyata." Sadam! yaji wani bala'in takaici ya kamashi jin abinda Talle ke fad'a ba wai yana kishi bane kawai tsabar kauyancin da sukeyi shine yake bashi haushi.....Bai iya ce masa komai ba ya kalleta tana tsaye sai tauna gefan dankwalinta take yace."Dauki kayan tallan ki wuce gida."! Shiru tayi tana kallonsa tare sa zu'baro baki. Kwata kwata baya son dukanta shiyasa ma kafin ya isa gurin ya saisaita tunaninsa domun a yanda zuciyarsa ke masa zafi da yarinyar yana gani zai iya yi mata mugun rauni saboda duka shiyasa taushi zuciyarsa akanta bayan haka kuma yanajin tausayinta saboda maraicinta gaba da baya. Talle yayi wani 'kas! da hannu irin na gayu na 'kauye yayi wani juyi da kafafunsa da suke sanye da wani fatattakaken kambos yace."Baby sai gobe zamu had'e naga wannan gayen shima kamar yana sonki to karki damu da komai baby tunda ni kike so nima ina sonki." Talle Ya fad'i wannan maganar ne domin ya cuzgunawa Sadam!! saboda a tunaninsa son Sayyadar yakeyi......Sadam! kam kallo ya bishi dashi cike da tsabar takaici ya ma rasa bakin magana ya dawo da kansa kanta "Dauki kayan tallan muje gida." "To ai gyadar bata 'kare b......." Wani bahagon mari ya kai mata! Allah yasa bai same ta ba don da ta sake marin nan ya same ta to sai tayi jini da majina! da sauri ta dauki farantin gyadar ta kama hanya tana waiwayen sa. Ya biyo bayanta cikin yanayi tafiyarsu ta sojoji. "Allah ya isa ban yafe ba mugu azzalimi d'an iska." ! Ire iren surutan da takeyi kenan tana waiwayensa Sadam! na gani tana motsa bakinta amma baya jin abinda take cewa saboda kasa kasa take maganar. Tana shiga kofar ta sa kuka a guje ta shiga ciki tana fad'in "Allah ya isa."!! Baba Ladidi! Kinga Ya Sadam! ya koroni ya hanani na siyar miki da gyadar ki kuma sai cini ki akeyi ya kori mutane." Baba Ladidi dake kishingid'e kan tabarma ta mike zaune tana gyara daurin dankwalinta tana kokarin magana ya shigo gidan. Kai tsaye inda suke zaune ya nufa ba tare da ya zauna ba yace."Baba ashe dama tallah kike d'orawa Sayyada yanzu don Allah me kika nema kika rasa da zaki dinga dora mata tallanta gyada da daddare tana shiga tsakiyar maza ke kin san sayyada ba nutsuwa ce da ita ba kike dora mata tallah." Tace."Haka kawai sai na zauna 'kuda yabi bakina ba zan nemi na kaina ba kenan? meye laifi don na dora mata tallah ai ko babu komai kudin cinikin yana toshe mana wata kafar saboda haka daukar tallah yanzu Sayyada ta fara idan kaga ta daina to tana dakin mijinta." Yace."A haka kike cewa in aureta kenan."!? Tace"Kwarai kuwa wai me kuke nufi ne? duk wanda zai ga Sayyada na zama gindi bishiya tana saida gyada sai ya fassara da wata manufar ni nasan halin sayyada baza ta aikata abinda kuke nufi ba ku kyale mu kawai mu nemi na kanmu." Cike da tsabar takaici yace."Babu rashin ci babu rashin sha babu rashin gurin kwanciya kike wata maganar, A gaskiya to kan wannan al'amari muna iya 'batawa dake domin wannan ba tarbiya bace da daddare kawai ki kasa mata tallah ta shiga cikin maza ke kina kwance a gida ba fata nake ba idan wata matsalar ta faru me zaki ce mana saboda haka kome zakiyi daga yau Sayyada ta daina daukar tallah." Baba tace"Sayyada ba zata daina daukar min tallah ba sai dai idan aure nayi mata wai ina ruwanku ne? kai kake wata magana idan kaji haushi yau ka turo sadakin auranta sai a daura muku aure ka dauke kayar ka amma matukar muna tare da ita baza ta daina tallah ba." Yace."Ai ni na gama magana ba zan aureta ba kuma tallah sai ta bari domin yanzu idan na fitar daga wannan kofar zan nufi gurin Sarkin 'kofa in shigar da 'korafina akanki." Ai sai Baba tasa kuka tana fad'in"Ni za ka kai 'kara gurin Sarkin 'kofa saboda baka da mutunci." Yace."To kece ai kin'ki ki zauna ki fahimci mutane kawai kina bin son zuciyarki." Tace."To naji zauna sai mu fahimci juna." Ya samu gefanta ya zauna tace"Maganar dai ta kare idan kana so sayyada ta daina tallah to ka yarda a daura muku aure kafin ka koma amma kar ka sake ka kai maganar gurin Sarkin 'kofa to kaji."! Yace."Shikkenan zanyi tunani kan maganar ki amma don Allah ko bayan na tafi karki 'kara dora mata tallah." tace"Haba ai magana ta 'kare bari na kawo maka abinci." Yace."Bari dai naje can kofar Kawu Tanko naci a can." "To babu laifi ai duk d'aya ne." Yana fita Sayyada tace"Baba yanzu da gaske kike kin daina soya gyada kuma na daina daukar tallah? kinga fa yau dari da ashirin nayi sannan Talle ya bar min sanjin talatin d'insa kinga d'ari da hamsin kenan." Baba ta kar'bi kudin tana lissafawa tace"Rabu dashi zai tafi ai sai mu cigaba da abinmu a kan wane dalili zasu hanani neman kudi." Sayyada tace"Nima dai abinda na gani kenan." Mikewa tayi taje ta zubo abinci ta zauna tana ci tana tunanin abinda ya faru tsakaninta dashi da safe duk sanda ta tuno da lokacin da ya dora hannunsa a kan nononta sai tsigar jikinta ta tashi wanda tunda suka fara fitowa bata taba jin wani yanayi a jikinta ba sai a wannan karon da sukayi ita dashi. **** Washe gari da safe dake tana riga kowa tashi a gidan Baba Ladi da Baba Marka na cikin dakin suna bacci ta share gidan ta had'e kwanuka ta wanke ta nufi bandaki domin ta wanke tana tura kofar bandakin lokacin shi kuma yana daure igiyar wandonshi karf suka had'a ido a razane! ta sauke idonta 'kasa ta saki kofar jiki na 'bari ta bar gurin....."Wayyo Allah wannan meye a mararshi kamar gashin jinjiri a kwance bakikirin a jiki dama haka jikin maza yake da gashi to me ya kawo gashi a marar sa. Jiki a sanyaye taje bayan Baba Ladi ta kwanta ta rintse ido tsigar jikinta sai tashi takeyi. Sadam! kam yaji takaicin ganin da tayi masa yana daure tazuge wato Allah ne ma yaso shi ya riga ya gama uzirinsa da yarinyar nan ta cuce shi.......Ya fito ya dauki brush dinsa inda ya aje ya goge bakinsa tsaf ya koma masaukinsa cike da takaicin yarinyar. 27/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Free Pege 5 Sayyada shiru tayi a bayan Baba Ladi tana zare ido rintse ido tayi sai kuma ta bud'e da sauri ta mike zaune ta hau sosa kai a hankali ta mike taje ta d'aga labule tana le'kensa yana goge bakinsa ta jima a tsaye a bakin kofa sai da taga ya mike tayi saurin sakin labulen ta dawo ta zauna tare da zabga tagumi tana tunanin abinda ta gani. Can ta saki ajiyar zuciya da taji tafiyarsa da alamu ya koma masaukinsa sai ta fito ta d'ibi ruwa cikin bokiti taje ta wanke bandakin.....Tana fitowa shima ya fito daga dakin da yake suka had'a ido tayi saurin dauke kanta tana gumtse baki dariya take so tayi amma tana jin tsoro. Sadam! ya girgiza kansa ya wuce dakin Baba bacci take sosai ya hau tashinta bude idonta tayi tana salati tare da hamma da alama tana jin dadin baccin yace."Baba ruwa nake so me zafi nayi wanka zan fita da wuri domin in zaga 'yan uwa kwana biyu kacal zanyi na koma." Baba Ladidi na d'aura d'ankwalinta tace"aikuwa babu ruwan zafi sai dai na dora maka idan na dama kunu." Yace."A'a ki fara d'umamin ruwan zafin kafin ki d'ora kunun." Tace"To haka za'ayi." Sai ta hau kiran Sayyada. Ta shigo tamkar wata mai hankali tace"Gani Baba." "Ki d'orawa Mijinki ruwan wanka." Jin abinda tace yasa ta zum'bura baki tare da fad'in"Kai Baba."! Mikewa tayi ta bar gurin. Duk suka bita da kallo yace."Wallahi baba ladi kina bani haushi wannan wace iriyar magana ce salon kawai ta raina ni yaushe na zama mijinta." Baba Tace."Yo kwana nawa ne kuma ai gwara in dinga kiranta da sunan matarka yafi armashi." Takaici yasa ya mike ya fito tsakar gida.....Tana tsugune can wani ke'bantaccen guri da suke girki tana kunna wuta a (kurfoti) ya tsirawa bayanta ido yana ayyana abubuwa da dama kanta shi yanzu ya auri wannan yarinyar ya auri me? yarinya babu fasali babu gaba babu baya sai uban tsayi kamar lisha shi yafi son mace mai brest da hips sosai duk da dai yarinyar bata gama girma ba amma yana ganin anya kuwa sai dai ya lura tana da shafaffen ciki da alama kuma zata yi hips masu kyau. Duk hannuwansa ya zura a cikin aljihu yana kallonta ta mike da wata butar 'karfe da suke d'umama ruwa taje ta ciko da ruwa ta d'ora kan wuta tana juyowa suka had'a ido. 'Kasa tayi da kanta tana kauda kai tazo zata wuce shi....Sai da tazo daf dashi sannan dariyar da take 'boyewa ta su'bce sai ta rife bakinta da tafin hannunta tana kyakyatawa, idanunta tsaye a kansa tamkar taga mahaukaci. Shan kunu! yayi sosai saboda ya fahimci abinda takewa dariya yace."Don Ubanki dariyar me kike? wa kika mayar mahaukaci anan gurin." Baba Ladi ta fito da sauri tana fad'in"A'a ya naji ana zagi kuma."!? Sayyada tayi bayanta ta 'boya tana ti'kar dariya Baba tace"Ke bana son ja'irci da shashanci dariyar me kikeyi haka."? Tana dai dariyar tace"Baba gashinan a tsaye shine ya bani dariya wai da girmansa yake tusa hahahaha! Allah baba ba kiji tusar tasa ba mai warin tsiya da 'kyar na wanke band'akin." Baba Ladi ta kama dariya tana tafa hannu ''Oh! ke kiji ja'irce na Sayyada a ina kikaga yana tusar."? Shiru tayi tana kallonsa tana dariya. Sadam! yayi tsai a tsaye yana kallonsu daga ita har Baban haushi suke bashi yana tunanin abinda zaiyi musu ya huce yarinyar nan Sayyada ta raina shi wai shi yake tusa mai wari amma dai yaji dad'i da bata fad'awa Baban cewa ta ganshi yana d'aure tazuge ba. Baba tace"Sadam! kaji d'an bukin da Sayyada take maka ko hummm ni nasan barkwanci ne kawai irin nata humm Sayyada kenan."!!!! Takaici bai barshi yace musu komai ba sai yayi shiru da bakinsa shiru ma magana ce dauke kansa yayi tare da kauda kansa ya murtuke fuskarsa. Yana kallon yanda ruwan ke turiri yasa ya mi'ke aikuwa ta zabura! da gudu tayi hanyar fita wai ta d'auka dukanta zaiyi......Karo suka buga da Amina tana dauke da wani dogon kofi mai murfi cike da 'kunu mai zafin gaske aikuwa duk kunan ya kware a jikinta inda ta fasa wani irin ihu! tana tsalle radad'i da zafi ya isheta. Amina ta jefar da kofin tayi kanta da gudu tana goge mata ita kuma sai kwara ruwa take a jikinta Baba Ladidi ta karaso gurin tana salati tare da fad'in"Garin Yaya haka ta faru!? maza-maza ki cire rigar kai!!! abu baiyi dadi ba. Yana tsaye daga inda yake yana kallonta tana kuka duk tayi wurjanjan da ita. Baba Marka ta fito daga d'akinta tana fad'in"Jama'a wai meke faruwa ne? nake tajin kuka da hayaniya? Taga Sadam a tsaye bai ce mata komai ba sai ta karasa inda suke tana tambayar ba'asi Baba Kadi ta fad'a mata abunda ya faru....Tace"Sayyada wannan guje gujen naki bashi da amfani kinga abinda ya jawo miki ko."? ''Ni fa Baba ki 'kyaleni kar kiyi min wannan mitar taki kawai ki kyaleni naji da abunda nake ji." Tafad'a tana 'kokarin zare rigar jikinta wanda ko 'yar shimi babu Ita kuwa Baba Ladidi sai taya ta take. Omar na ganin sun sa'bule rigar ya d'auke kansa da sauri sunkuyawa yayi ya d'auki ruwan zafinsa dake kan wuta ya kama hanyar bandaki.....Yana kauda kai ya isa inda suke tsautsayi yasa ya d'aga kansa aikuwa karaf! kan 'kananun brest d'in Sayyada da suke a tsaye kamar agwalima tas tas dasu shatin nipples din yayi baki abinka da farar fata....Tsigar jikinsa ta mi'ke yarrrr! cikin rashin hayyaci ya isa bakin rijiya ya ja ruwa ya sirka da sauri ya dauka ya shiga bandaki yana jin yanda gabansa ke harbawa alamun lafiya da kuma alamun sha'awar shi ta motsa. Cikin dauriya yayi wankan ya fito da fuska a daure ko da ya fito sam! bai kalli inda suke ba ya nufi dakinsa domin kintsawa. Baba Marka tace"Wannan dai sashanci ne Sayyada ki dauki rigarki ki mayar haba ai be dace ba ki cire riga alhalin kin san kin soma girma sai kace wata yarinya karama." Baba Ladidi tace"A'a Marka 'konewa fa tayi kike cewa tasa riga mu bari dai gurin ya sha iska tukkuna idan rigar zata sai ta sa amma ba yanzu ba." Marka tace"aishikkenan." Wucewa tayi dakinta ita kuma Amina ta dauko jug din ta fita Sayyada da Baba Ladi suka nufi daki Baba Ladidi na cewa "Zuwa anjima idan ba ta daina yi miki rad'adi ba sai muje gurin tofi." Sayyada ta samu guri tayi rashe-rashe a tsakar da'ki kirji a bud'e saboda tsabar sangarta wai ita ta 'kone. Baba Ladi ta fito ta d'ora musu kunu tana fad'in"Yau dai babu halin siyo mana kosai kenan dole in dauki mayafi inje da kaina bari dai na d'ora ruwan kunun." Kullum daga 'bangaran Baba Tanko ana kawo musu kunu da yawa amma saboda rigima irin tasu ta tsofaffi sai suce sai sun dama da kansu Kawu Tanko da kansa yake siyo musu kosai iya inda zai ishe su amma sai sun kara siya idan yara sun shigo suyi ta raba musu, ganin yana wahalar da kansa yasa ya daina siya musu kosan shine suke bawa Sayyada na siyo musu kullm da safe. Baba Marka ta fito da lullu'bi a kanta tace"To tunda kin d'aurewa 'yar aiken tamu gindi sai muje siyo kosan da kanmu." Tace."Marka kenan ba daure mata gindi nayi ba ni nasan sharrin 'konuwa shiyasa nace ta zauna babu riga yanzu tana iya saka rigar 'kunar tazo ta tashi kinga yanzu wa gari ya waya gwara a bari tasha iska tukkuna." Baba Marka tace",To ashikkenan ni da ina ganin hakan bai dace ba tunda Sadam na gidan kinsan fa shi Namiji baya raina abu." Ladi tayi dariya irin tasu ta tsaffi tace"Haba Marka kamar ba shi zai aure ta ba ai ba laifi bane kuma ba da gangan ta cire rigar ba, tsautsayi a ka samu." Marka tace"Hakane kuma." Tace."Bari in dauko mayafi na muje gurin Tabawa me kosan." Ladi ta yafa mayafi suka kama hanya suka fice daga gidan wai sun tafi siyo kosai. Tsaf ya fito cikin kufta na yadin Kashmir yayi kyau sosai bai sanya hula ba saboda ba ma'abocin ta bane sai dai ya gyara sumarsa sosai sai kamshi yake mai dadi, jin gidan shiru yasa ya nufi dakin Baba Ladidi. Al'marin yazo masa a bazata! yana d'aga labule ya ganta tayi wata iriyar kwanciya bacci ma takeyi. Tsira mata ido yayi yana kallonta tas ya kare mata kallo sama da 'kasa ba kirjinta dake waje ba har dan pant dinta sai da ya hango sakamakon kwanciyar da tayi. Rai a 'bace ya bude baki yana kiran "Baba Ladi.'! Shiru yaji ya saki labulan da sauri ya bude dakin Baba Marka bata nan da alama tare suka fita. Tsakiyar tsakar gidan ya tsaya yana tunani, tsaki yaja ya sake daga labulan dakin Baba Ladidi tananan inda take sai kawai ya shiga dakin ya tsaya a kanta. Sayyada cikin bacci taji kamar motsi a kanta ido ta bud'e ta ganshi tsaye sai tayi saurin mikewa tana zare ido sai sannan kuma kunya ta kamata ganin kirjinta a bud'e sai ta jawo dankwali zata rufe ya fuzge dankwalin yana me tsira mata lumsassun idanunsa. Hawaye ya fara zubo mata daga ido......" Rufe min baki dan Ubanki."!Ya fada tare da kauda kansa. Hannu tasa ta rufe bakin. Yace."Mekenan hakan da kikayi."? shiru tayi yace."Ke bakya kishin kanki wai! duba ki gani kin kwanta babu riga ba kya tsoron wani ya shigo yaga jikinki dan Uwarki ko 'yar uwarki mace ta ganki a haka ai ta cuce ki bare kuma namiji wani ma danne ki zaiyi duk da 'kananun shekarunki." Tana Hawaye tace."Amina ce fa ta kwara min kunu a jiki kuma duk nan d'ina ya 'kone shine Baba tace "na zauna babu riga 'kunar tasha iska."! Harararta yayi tare da ya mutsa fuska yace." Ai dake da Babar ban san wanda yafi wani hauka ba, duk abinda ya faru ai kece kika jawowa kanki da guje gujan ki na banza da wofi ko ba dariya kike min ba."? Shiru tayi tana kare kirjinta da hannu ya d'auke hannunta daga gurin yana fad'in"Me kike fufewa bayan na gama gani." Kauda kai tayi sai kawai ya sanya hannu ya murd'e! nipple d'aya cikin a zabah! ta kwallara 'kara zata mi'ke yace."Koma ki zauna."!!!! Jiki na kyarma! ta koma ta zauna tana fad'in"Don Allah Ya Sadam! kayi hakuri kaji."! Cikin sigar bagararwa yace."Me kikayi min da zaki bani hakuri."!? Cikin rashin wayo da dubara tace"Na le'ka ka kana bandaki." Harara ya watsa mata yace."Don Ubanki da kika le'ka me kika gani."? "Wallahi banga komai ba." Tafada tana d'aga hannunta. Murmushin mugunta yayi yace."To me yasa kike min dariya ko ni d'in mahaukaci ne."!? Girgiza kai tayi tana hawaye. Ya tsirawa brest din ido sunyi wani cibir dasu sun burgeshi kwarai ya'ki kawai yake da zuciyarsa kar tasa shi aikata abinda ba shikkenan ba, Yace."Ki kiyaye ni wallahi ni nan ba Yaya Sule bane marainin wayon ki kin san halina kikayi min shirme zan ci Ubanki ne kuma in kwana lafiya don haka ki kiyaye." "Tace" Kayi hakuri." Shiru yayi tare da mi'ka hannu zai kama breat din ta zabura! tare da 'kam-kame jikinta gurin guda. Yace."Dallah Malama tsaya duba miki gurin 'kunar zanyi." Sai ta saki jikinta tana kallonsa ya d'ora hannu akan duk brest dinta yana latsawa wannan karon bada mugunta yake ba a hankali yakeyi yana shafa brest din yana murza nipples din ajiyar zuciya ta sauke! ta tsira masa ido tana kallonsa shima ita yake kallo cikin wani irin yanayi mara misaltuwa yace."Ina ne gurin."!? Ta d'auki hannunsa tana d'ora 'kasan brest din inda kunun yafi zuba murya a sanyaye tace."Nan ne."! Shafa gurin yayi sai ya fara motsi da bakinsa da alama addua yakeyi ya gama ya tofa a hannunsa ya shafa a gurin.....A hankali ya cire hannunsa daga gurin yace."Dauki rigar ki kisa. Babu Musu ta d'auki rigar tasa tana kallonsa ya fita daga dakin sai ta koma ta kwanta tana takurewa.......Shi kuma yana jin motsin shigowae su Baba Ladidi sai yayi saurin shiga dakin tare da sayo 'kofa zama yayi kan katifa tare da dafe kansa. 27/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Free pege 6 Baba Ladi ta daga labule dakin ta shiga da sallama a bakinta. Sayyada ta bude lumsassun idanunta ta amsa tana kokarin mikewa zaune Baba ladi ta sami guri ta zauna tana fad'in"Ki tashi kisha kunun ga kosai na siyo mana yau gurin marka babu jama'a sosai shiyasa na dawo da wuri." Sayyada ta mike zaune tana mutsika ido Baba Ladi ta bita da kallo tace"bacci kikayi ne naga duk kin sauya lokaci kankani." Sayyada ta sunkuyar da kanta girgiza kanta tayi ba tace komai ba. Baba Ladi bata kawo komai cikin ranta ba tace "Idan kin karya sai ki kwanta naga alama bacci kike ji." Ita dai Sayyada ba tace komai ba kwata kwata ma bata cikin nutsuwarta tun bayan fitarsa daga dakin. Mazubi ta samo ta d'ibar masa kosan tana nufin shiga dakin shi kuma ya fito tace"Ina zakaje kuma ga kosan na kawo maka." A dakile yace."Zanje can sashen Kawu Tanko na karya a can." Ya kama hanyar futa Baba Ladi ta bishi da kallo tana gyda kai har sai da ya fita daga kofar ta dauke kanta tana girgiza kai tare da fad'in"Miskili kenan." Kofar Kawu Tanko ya nufa lokacin Kawun tuni ya tafi gona suka gaisa da Baba Iyatu Amina ta fito daga daki a nutse ta gaisheshi ya saki fuska yana amsawa tace"Yaya Sadam! jiya kace zaka duba litattafai na makaranta." Yace."Na manta ne amma yanzu jeki dauko in duba miki." Ta mike da sauri ta nufi daki. Baba Iya tace"Kafin ku fara karatun bari in kawo maka kunu ka karya ko ayi maka wani abincin ne."!? Yace."Kunun ma ya isa Baba." Tace."To." a cikin mazubi mai kyau ta kawo masa kunun tsamiya sai kamshi yake gwanin sha'awa gefe guda kuma ga wainar gero cikin wata Samira taji kuli-kuli tayi kyau. Yace."Gaskiya Baba naji dadin wannan wainar na kwana biyu rabona da inyi irin wannan karin kummalon." Baba Iya tace"Ai dama ku mutanan birni bakwa damuwa da cima irin wannan amma tafi gina jiki da kara lafiya." Yace."Gaskiyar Baba." Hira suke da ita har ya kammala karyawa Amina ta dauko jakar makarantar ta ya duba sosai ya yaba da kokarin ta nan ya rasa kyautar da zaiyi mata yace."Me kike so na siya miki."!? Mirmushi tayi yace."Ki fada mana aini nayi miki alkawari zan baki kyauta." Tace."Ni kam Yayana kome ka bani ina so." Yace."Sai kin fadi me kike so kayan kwalliya ko zani ko mayafi."!? Girgiza kai tayi yace."okey fadi me kike so." Hannunsa ta kalla tana nuna wata siririyar azirfar dake hannunsa sai she'ki take. Tace"Wannan zoben nake so kabani yana bani sha'awa." Yayi tsai! yana kallonta na minti biyu yace."Wannan azirfar tawa tana da muhimanci Amina ki za'bi wani abun bayan ita." Sai ta girgiza kai tace"Shikkenan kawai ka barshi." Murmushi yayi yace."Bani hannunki na sa miki." Ta matsa gurinsa da sauri tana dariyar farin ciki Azurfar ya ciro ya kama hannunta ya fara gwadawa duk tayi mata yawa dake Amina bata da wata 'kibar arziki haka ya tsunta ma suke sirara yace."Kinga tayi miki yawa ko." Dariya tayi tace"Kasa min a wannan hannun zata shiga." Sai ya kama hannun da ta nuna masa yana gwadawa......Sayyada ta shigo dakin taga abunda suke tsayawa tana kallonsu ta 'bata rai!!! fuuuuu! ta fice daga dakin tamkar zata fashe! duk suka bita da kallo Ta'be bakinsa yayi ya cigaba da abinda yake. Sayyada kam da kuka ta shiga kofar su Baba Ladidi na shimfida tabarma ta tsaya tana tambayarta abinda ke faruwa. Cikin kuka tace"Baba Nifa ban gane ba kunce Yaya Sadam! ni zai aura to me yasa naga kamar yana son Amina wallahi ni bazan yarda ba sai dai ta hakura ta bar min mijina." Baba Marka ta fito daga dakinta tana fadin"Wace magana nake ji haka."? Baba Ladi tace"To nima dai yanzu nake jin maganar gurin Sayyada wai me ya faru ne Sayyada."!? Tace"Yanzu na shiga kofar su naga yana sa mata zoben al'kawari a hannu kawai ya fito ya fad'i gaskiyar magana ni yake so ko Amina."!? Baba Marka tace"To aikuwa dai wannan maganar abar dubawa ce Sayyada bari na shiga inga abinda yake faruwa babu shakka Sadam yana nema ya mai damu kananun mutane."! Baba Marka na fita Baba Ladidi tace "Zauna muyi magana Ta zauna tana share hawaye Baba Marka tace" Sayyada yanzu idan Sadam! yace zai had'aku ya aura da 'yar uwarki ashe ba zaki zauna da ita ba ko."? Wallahi baba ba zan zauna da ita ba sai dai ya za'ba ni ko ita shikkenan." tsakaninta da Allah take maganar. Baba Ladidi tayi shiru tana nazarin maganar lallai akwai matsala kenan. Yanzu idan Sadam! Amina yake so za'a samu matsala daga 'bangaran Sayyada kenan al'kwarin dake tsakaninsu zai iya rugujewa tunda shi Sadam! din yana da kafewa akan magana. Baba Marka na shiga ta tarar dasu suna hira cikin fahintar juna cikin zuciyarta tace"Babu shakka, da gaske Sayyada takeyi. Ta zauna kan kujera 'yar tsuguno tace"Kai Sadam! fito nan zamuyi magana." Yace."Yanzu dama zan fito ina so in le'ka cikin gari gurin 'yan uwa za muje tare da Amina." Tace"To babu laifi ai ke Amina kema zonan." Suka fito tare tsugunawa yayi a gefanta amina kuma ta zauna kan tabarma. Baba Marka tace"Ina so ku fad'a min abunda yake tsakaninku bana son munafurci kai Sadam! duk kaine me laifi." Yace."Baba ban fahimci maganar ki ba."!? Tace"Sayyada taje mana da wata magana shin da gaske ne kasawa Amina zoben al'kawari kana so ka aureta ne ko yaya."!? A take yayi kicin-kicin da fuska yace."Wannan wace iriyar magana ce Baba."!? Tace"Magana ce me mahimanci shin tsakanin Amina da Sayyada wa kake so kana kokarin kayi mana wasa da hankali." Kai tsaye yace."Cikin su babu wacce nake so."! Baba Marka ta bud'e baki tana kallonsa cike da mamaki tace"To wannan zoben da kasa mata fa na menene."!? Yace."Kawai nayi ra'ayi ne ba na komai bane Sayyada da Amina babu wacce nake jin zan aura a cikinsu duk na daukesu a matsayin 'yan uwana ne. Baba Marka tace"Aikuwa baka isa ba sai ka auri daya daga cikinsu." Miskilin murmushi yayi ya mike yana kallon agogon dake daure a hannunsa yace."Baba naga alama zan daina shigowa garin nan mutukar zaku cigaba da damuna kan wannan maganar wai shin ni kadai ne namiji a wannan family din gasunan da yawa amma sai kuyi ta takura min da wata magana! Ke Amina tashi dauko gyalanki mu tafi ni duk garin ma ya fice min daga rai."! Yafada yana zura takalminsa. Baba Marka tace"Ai komai zakayi sai dai kayi kana maganar ga Samari nan a famly ko wanne yana da matarsa a hannu kai kadai ne kayi shaura bakayi aure ba sai kace kuma mu zuba maka ido to baka isa ba to kaji."! Yace."Sai kuyi ai." ! hanyar fita ya nufa Amina ta bi bayansa tana sanye da hijab har kasa takaici duk ya isheta da jin maganar sa inda yake cewa baya sonsu ita da Sayyada. Sayyada na zaune a bakin kofar su suka fito tana ganinsu ta 'bata rai!! ko kallonta baiyi ba ya nufi babbar 'kofar da zata sada mutum da kofar gidan.....Amina tabi bayansa cikin sanyin Jiki. Cike da takaici da bakin ciki ta bar gurin kan gadon karfen Baba Ladidi ta kwanta ta dinga kukan bakin ciki tana bala'in son Yaya Sadam! shiyasa bata son kowa ya ra'be shi ta lura kuma shi ya tsaneta kamar yafi son Amina akanta. **** Sai Yamma li'kis! suka dawo gida Sadam? sam bai shiga ciki ba sai yayi zamansa a majalisar Samarin garin inda ya saba zama idan ya shigo garin sai kusan tara da rabi na dare ya shigo gidan......Dama yayi zuciya yace ba zai kwana bangaran su Baba Ladidi ba saboda yasan zasu takura masa sai ya nufi kofar Kawu Tanko yana sanya kafar sa ya hango Sayyada jikin kyaure('kofa) tana tauna gyalanta shi kuma saurayin yana tsaye a kanta, kamar ma zai rungume ta gabansa ya fad'i! da sauri ya dawo da baya kai tsaye ya nufi inda suke. Yana isa yaji muryar ta tana fad'in"Nifa ba wai bana sonka bane kawai an riga anyi min miji dan uwana ne don haka kayi hakuri don Allah yanzu ma Baba Ladidi ce tace nazo na baka hakuri ka daina zuwa zance."! Talle ya cire hular dake kansa yana fifita da ita yace."Haba baby ai al'kawari bai ce haka ba ki duba lamarin da kyau ki tausayawa masoyink......Kafin ya karasa suka ganshi a tsaye a kansu fuskarsa kamar hadarin da yake daf da zubar da ruwa. Sayyada tasha kunu! har yanzu haushinsa takeji kuma tayi al'kawarin sai taci mutuncin Amina tunda ta shiga gonar ta. Talle ya kalleshi she'keke babu shakka shine wanda Sayyada take fada mijinta......Sadam! yayi musu wani irin kallo yana ya tsine fuska saboda yanda yake jin tsamin daud'a had'e da warin hammata ya cika gurin zuciyarsa har ta fara tashi miyau ya tsartar! ya d'auke kansa kwata kwata baya son kallon Talle saboda yanda yake hango wani bushashshan tasono a 'kofofin hancin sa abun 'kyamkyami! sosai yayi mamakin yanda akayi Sayyadar ta tsaya a gurin har take sha'kar wannan warin. A murtuke yace."Kai Malam kama hanya ka tafi hirar ta isa haka ko baka san dare yayi bane uhum!? ya kalli Sayyada dake cin kunu yace."Ke kuma shashasha! kin tsaya kina sha'kar wannan mugun warin sai ya d'aure miki ciki ko da yake dake dashi duk d'aya kuke kema 'kazamar ce."! Tace."To ina ruwanka damu."! "Eh babu ruwana daku ai ban ce wani abu ba masoya cewa nayi dare yayi ke ki shiga gida shi kuma ya tafi gida sai kuma gobe."! Talle yace." Kaga Malam babu ruwanka damu ya muna soyayya zaka shiga tsakaninmu shin kai kuwa kasan menene so kuwa."!? Sadam! ya saki wani murmushi na takaici yace."A'a ban sani ba sai kai Laila majnun! ko zaka koya min ne guy."! Talle yayi wani juyi yana fad'in"In kana so sai a ko ya maka." Tsaki yaja yana ya mutsa fuska yace."Sayyada wuce ki shiga gida." Zum'bura baki tayi tace"Ni ka kyaleni nayi zance na kai ma ba d'azu kayi da Amina ba to menene zakace dole sai na shiga gida." Ransa ya 'baci wato don taga yana lalla'ba ta shine zata kawo masa raini sai ya murtuke fuska yace."Wallahi zan mareki kika kara wata magana anan gurin wuce ki shiga gida." 'Kin shiga tayi sai ma ta dinga matsawa jikin Talle tana tauna gyalanta sai kace yarinya karama.....A fusace! ya jawo ta zai gaura mata mari Talle yayi caraf! ya ri'ke hannunsa "Kai kar ka kuskura ka dok......... Kafin ya 'karasa yaji wani irin azabar rad'ad'i! a hannunsa Sadam! ya murd'e masa 'yan yatsu har sai da suka bada sautin 'kas!'kas!!!! Ihu!!! yayi a take idanunsa sukayi jawur! saboda azabah! fitsari ne kawai Talle bai saki ba.....Sadam! na sakar masa hannu ya kama hanya ya fice da sauri ko waigowa baiyi ba. Sayyada na ganin ya juyo kanta...Sai ta shige cikin gidan da sauri tasan halin sa sai ya mareta gashi marinsa zafi ne dashi takan kwana biyu tana jinyar fuskarta. 28/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Free pege7 Ko lokacin da Sayyada ta shiga ciki Baba Ladidi da Baba Marka duk sunyi bacci a tsakar gida da yake lokacin zafi ne nan suke kwanciya sai asubah suke komawa d'akunansu, kai tsaye daki ta shiga domin dauko bargon da take kwanciya taji masifar dadi da Sadam! ya ga Talle suna zance yasan itama ba samari ta rasa. Tana fitowa daga dakin suka ci karo dashi ya shigo sai tayi saurin komawa da baya gabanta na faduwa ta dauka ai yayi tafiyarsa. Cikin uwar dakin ta shiga ya bita sai ta soma ta'be fuska zatayi kuka ya daka mata wata iriyar tsawa! shiru tayi tana kallonsa. "Wallahi duk sanda na kara ganinki a tsaye da wannan 'kazamin sai ranki ya 'baci ke ki rasa wanda zaki tsaya dashi sai wannan shashashan mai warin d'auda."! " To ina ruwanka dashi ni shi naga ni kuma shi nake so."! Mari ya kai mata ta kauce! da sauri ta tsorata da ganin yanayinsa. Yace."Saboda baki da kunya ina miki magana kina mayar min kin raina ni ko."!? Da karfi ya fadi maganar. Shiru tayi yace."To ki kuskura na gani ko naji labarin kin sake tsayawa dashi wallahi sai na dauki mataki mai tsauri a kanki zan sanya matakan tsaro sosai a kanki." Tana kuka tace"Wai kai ina ruwanka ne? kaine fa kace ba zaka aure ni ba sai kuma ka hanani kula Samarina ai ba zai yiwu b......Ya kaiwa bakinta duka da sauri ta rufe da hannunta ya daki hannun ta sake fashewa da kuka mai karfi wanda yayi sanadiyar tashin Baba Ladi daga bacci....."Ke! Sayyada menene kina ina ne."!? baba ladidi ke wannan maganar tana haska karamar toch inda sayyada ke kwanciya sai taga gurin wayam! tana kokarin mikewa Sayyadar ta fito daga d'akin a guje bayanta ta 'buya tana kuka Ya fito daga dakin yana wani irin huci! na bacin rai! Baba Ladidi ta haske shi da fitila tace"Wai menene? Bafa nasan neman fitina me tayi maka."? Yace."Baba kina kwance da kina bacci yarinyar nan ta fita da daddare tana zance da wani d'an iskan yaro kazami! duba time goma na dare har ta wuce." Baba ta kalli Sayyada dake tsaye tace"Wato da kikaga nayi bacci shine kika fita zance ko wai ke Sayyada me yasa bakya jin magana ne."!? Tana kuka tace"To Baba ai ba laifi nayi ba shima yana zance da wata kuma ai har yanzu bai tabbatar muku da cewar zai aure ni ba to kawai sai a hanani inyi zance." Baba Marka dake kwance ta mike zaune tana fad'in" Yanzu ke Sayyada me zaki ci da wannan yaron Talle bai aje ba bai bawa kowa ajiya ba haba kiyiwa kanki fad'a mana, koda Sadam! bai aure ki ba Talle ba sa'an auranki bane saboda duk gari kowa yasan ba yaron arziki bane ko ya aure ki ba zaki samu kyakkyawar kulawar da muke so ba." "To ni dai shi nake so A kyaleni kawai." Tafada tana goge fuska....Sadam! yace."Shikkenan Baba ku rabu da ita tunda shi take so sai a daura mata aure dashi ni idan Allah ya kaimu gobe kafin in wuce zan samu iyayensa sai a tsayar da magana." Sayyada gabanta ya yanke ya fad'i!!!! da jin abinda yace cikin zuciyarta tace "Allah yasa ba da gaske yake ba lokaci kankani jikinta yayi sanyi. Baba Ladidi tace" Shikkenan ni na cire bakina daga wannan sabgar tunda dai kin nuna mana cewar kin fi son ki auri Tallen shikkenan, kai Sadam! idan Allah ya kaimu gobe da wurwuri sai kuje da Kawunka ku fara maganar auran Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Ya kama hanya futa Baba Marka tace"Yau ba anan zaka kwana bane."!? Yace."Eh can sashen Kawu Tanko zan kwana." Tace"To Allah ya tashemu lafiya." Ba tare da ya amsa ba ya fita. Sayyada tayi tsuru a zaune Baba Ladidi da Baba Marka suka gyara kwanciyarsu ko wacce ta cigaba da baccin ta suka bar Sayyada da tunanin ya zatayi ta fitar da kanta. Juyi kawai takeyi ta kasa bacci ga gari yayi duhu sosai kowa yayi bacci da alama ma sha biyu ta wuce sai dai karfe daya kuma, mi'kewa tayi a hankali ta lalla'ba ta fice kai tsaye 'kofar Kawu Tanko ta nufa......Shiru kowa yayi bacci ta lalla'ba ta nufi dakin da take tunanin yana ciki aikuwa takalmanshi ta gani kofar a bud'e amma ya sayo ta ta tura ta shiga babu fargabar komai a tattare da ita. Yana kwance kan katifa da wayar a hannunsa yana dubawa da alama wani abu mai muhimmanci yake dubawa yana sanye da vest fara sai gajeran wando kirjinsa da abinda yayi cinyoyinsa zuwa 'kasa wani irin gashi ne akwance da alama mutum ne shi mai gargasa a jiki ko ga yanayin sumar dake kansa zaka gane. Da sauri ya mi'ke zaune ganinta a tsaye a kansa ya kunna hasken wayarsa yana haske fuskarta. "Ke! Lafiya."!? yafada cikin mamaki.! Wasa ta farayi da hannunta ta jawo jelar dankwalinta tana taunawa, haushi ya isheshi saboda yanayi na dare yasa ya taushi zuciyarsa yace." Wai ba dake nake magana ba me ya kawo ki nan."!? Zubewa tayu gwiwa bibbiyu ta fashe da kuka! A razane! ya mike isa inda take, tura kofar dakin yayi sannan ya dawo inda take ya mikar da ita tsaye tare da toshe mata baki da hannunsa guda, hannunta yaja suka isa bakin katifar ya zaunar da ita kusa dashi har yanzu hannunsa na rufe da bakinta ya kura mata ido yana kallo itama shi take kallo da ido yake mata magana ta gane abinda yake nufi sai tayi kokarin had'iye kukanta sai da ya tabbatar tayi shiru sannan ya bude mata baki. A miskilance yace."Menene."!? Shiru tayi tana turo baki yace."Ke yanzu kawai sai ki shigo min daki kina kuka kawai saboda ki jawo min magana ko sharri kike so kiyi min."!? Girgiza kai tayi, Yace."To kan wane dalilin kike kuka kuma me kike so nayi miki cikin dare kika shigo min daki." Cikin kuka tace"Nifa ba cewa nayi kaje gidansu Talle ba na fasa auransa." Shaf ya manta da maganar mana Yace."Wannan dalilin ne yasa kike kuka."? daga kanta tayi yace."Me yasa to ba kyajin maganar magabatanki."? Shiru tayu tare da sunkuyar da kanta Yace."Tunda dai aure kike so to za'ayi miki insha Allahu."! Ta kalleshi da sauri! Sai ya d'aga mata girarsa guda ta mai da kanta kasa yace."Ko ina da wata magana."!? A hankali tace."To kai ba zaka aure ni ba."! Yace."Dama ai bance zan aure ki ba su Baba ne suke maganarsu bana sha'awar auran zumunci." Sai hawaye ya fara zubo mata ta mike tsaye shima ya mike fuskarsa a daure yace."Idan zaki daina kuka da damuwa ki daina Aure kamar anyi miki da Saurayinki anyi an gama." Tace."To sai me? ai shima mutum ne."! kofar dakin ta bude ta fita tana kuka ranta in yayi dubu ya 'baci.! Murmurshi yayi ya koma ya kwanta ya cigaba da abinda yake. Washe gari ya tashi da wuri ya tashi ya shirya tsaf ya nufi sashen su Baba domin su gaisa.....Lokacin da ya isa sashen suna karya kummalo Baba Marka ta shimfida masa tabarma ta kawo masa kayan karin kummalo ya karya Baba Ladidi ta fito da mafici a hannunta ta zauna kan kujera 'yar tsuguno tana fad'in"Ashe ka shigo." Yace."Eh Baba." Gaisawa sukayi yace."Kina fiffita da safe sai kace wata mara lafiya." Tace"Aini jin zafi ne dani bana rabo da mafici Tace."Ina fatan dai kunje gidan Su Talle kunyi maganar." Yace."Sai na k'ara dawowa za muje." Tace."Ai shikkenan to Allah ya kara dawo da kai lafiya." Yace." ameen. Suna nan zaune ta fito daga dakin cikin hijan na makaranta isilamiyya ta jakar buhu a rataye a kafadarta ko kallonsa ba tayi ba tace"Baba ni na tafi." Baba Marka tace"Kina kallon Sadam! kin wuce ba tare da gin gaishe shi ba." Banza tayi mata tayi tafiyarta." Baba Ladi tace"Ki kyaleta kawai kina ganin ko karyawa ba tayi ba zata fita jiya ma ba tayi wani baccin arziki ba saboda an hanata soyayya da Talle." Baba Marka tace"Ni dai banga abinda Sayyada zata ci da Wannan yaron ba." "To ai tunda shi ta za'ba zata aura shikkenan Allah ya sanya alkairi." Sadam! na jinsu suna zancen su uffan bai ce musu ba har ya gama karyawa kana yayi musu sallama ya kama hanyar Kaduna. 29/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Free pege 8 *Asalinsu* Jauro mai shanu shine mahaifin Alhaji Inuwa da Kawu Tanko sai baba Indo wacce Allah yayi wa rasuwa shekaru goma da suka wuce lokacin Sayyada nada shekaru hudu a duniya yanzu in an hada duk tana da shekaru goma sha hudu a duniya. Malam Jauro mai shanu yana da mata biyu Baba Ladidi da Baba Marka wanda rana d'aya aka d'aura masa auransu suka tare a rana daya....Shekara nayi Baba Ladidi ta haihu inda ta haifi da namiji aka sanya masa sunu Auwalu sai da Auwalu ya shekara bakwai sannan baba marka ta haihu itama namiji ta haifa Aka sanya masa suna Haruna dake sunan mahaifin Malam Jauro ne sai suke ce masa Tanko.....Bayan shekaru uku Baba Ladidi ta haifi mace Aka sanya mata Aisha suke kiranta da Indo Tsakanin Marka da Ladidi suna zaman lafiya sosai da sosai ta inda yaransu basa gane cewar wacece mahaifiyarsu a ciki zaman lafiya da kwanciyar hankali suke inda har jama'ar garin suke sha'awarsu suke kuma kwatance dasu. Dai-dai gwargwado Auwalu da Tanko sun samu ilimin addini dana boko sai suka soma har kokin noma da kiwon shanu da sauransu dake Auwalu mutum ne mai kuzari da zafin nama sai ya yanke shawarar fita daga garin nasu neman shekarar da sukayi aikin shinkafa ya cika mota guda ta a kori kura ya nufu kasuwar kano kasuwar (dawanau) ya sauka jama'a suka rufe shi kafin kice kwabo shinkafar da ya sauka da ita ta kare kimanin buhu talatin 'yan sari duk sun siye a take ya had'o kan kudinsa ya nufo gida suka sake aikin wata shinkafar ya sake dauka ya nufi garin kaduna anan ma dai shinkafar ba tayi wani tasiri ba suka siye tas....Kafin kice kwabo likkafa ta cigaba harkoki suka budewa Auwalu ya dinga bin gari gari yana sauke musu shinkafa mai kyau suna siya.......Cikin garin kaduna ya hadu da matarsa wacce ta kasance itace uwar 'yayansa Fatsima sunanta, ko da ya sanar da iyayensa cewar ya samu matar amma ba 'yar dangi ba bace can garin Kaduna take sai suka nuna amincewarsu sukayi masa fatan alkairi ba'aja wani dogon lokaci ba aka daura aure tare da amincewar su. Allah ya albarkaci auran kawarai da gaske Arziki da wadata suka sake suke 'karuwa shekara na zuwa duk ya biya musu kudi sukaje suka sauke farali Dashi da Mahaifinsa Jauro da kuma baba ladidi da baba marka da Indo sai da dan uwansa Tanko da matarsa, addua ta ko wane fanni Alhaji Auwal ya samu ya gina gida mai kyau da kayatuwa sannan ya dawo garinsa na gado *Dabi* ya gyara musu dai-dai gwargwado ya zube musu abubuwan more rayuwa.....Tanko shike kula da harkokinsu na noma na garin.....Shekara daya da zuwansu aikin hajji Hjy Fatsima ta haihu inda ta haifi d'a Namiji aka sanya masa suna Sulaiman.....Malam Jauro da iyalinsa suka zo suka ga jinjiri suka sanya masa albarka. **** Auran Kawu Tanko da Baba Indo a rana daya aka daurashi Kawu Tanko auran zumunci yayi inda ya auri 'yar gidan Dantani wanda ya kasance 'kani na jini da Malam Jauro Baba Iya itace matar Kawu Tanko asalin sunanta Hamara'u Baba Indo kuma ta auri d'an gidan Maigarin garin *Dabi* mai suna Qasimu, ta zauna a cikin gidan mai gari dake gidan mai girma ne sosai bangare guda aka ware mata a cikin gidan. *** Sulaiman nada shekaru hudu Hjy Fatsima ta sake haihuwa inda ta sake haihuwar Da namiji lokacin ne aka rigima tsakanin turawa da salihin mutumin nan da ya baiwa addinin musulunci guduma wato *Sadam! Hussain* a ranar da aka haifeshi aranar aka kashe Sadam! don haka sati na zagayowa Alhaji Auwal ya sanya masa suna Sadam! Saboda duk wani musulimi a wancan lokacin yaji ciwon abinda kafirai suka aikata kan mutumin nan duk mai kishin musulunci dole sai ya jajanta al'amarin. ******* Sadam! tunda ya taso yake da wani irin hali mutum ne mai gudun zuciya da tsantseni yana da tsafta sosai kuma miskili ne sam baya son wasa idan kagan shi tare da d'an uwansa sai ka dauka shine babba saboda Allah yayi masa kwarjini da haiba dukanin family dinsu babu ba'ki sai shi dukaninsu farare ne kyawawa daga mazan har matan hanci har baka ga uban gashi shi kadai ne 'baki a cikinsu amma kuma a zahirance yafi su kyau sai wanda ya zauna dashi zai fahimci hakan kyakykyawa ne mutuka yana da manya idanu wanda suka dan risina kadan kewayayyiyar fuskar ta kawatu da wani saje mai kyau da tsari kasan ha'bar sa da saman bakinsa yana yawan yin gyaran fuska saman goshinsa akwai wani abu da yayi duhu tabon sallah kenan Sadam! yana da ibadah da kula da addini tun yana dan shekara goma sha hudu ya sauke al'kur'ani mai girma kwataa-kwata ba tsarinsu d'aya da yayansa Sulaiman ba wanda shi ya kasance mutum mai a'kidun turawa kaf karatunsa akasar waje yayi yanzu haka yana aiki 'karkashin hukumar tsare birni da kewaye na jahar Kaduna Sulaiman yana ta'ba siyasa sa'i da lokaci don har takarar dan majalisa ya tsaya Allah bai bashi ba. *** Sadam! kam tunda ya kawo 'karfi yaji yana sha"awar aikin soja don haka kawai sai ya sanja shawara ya shiga makarantar horar da sojoji dake Kaduna ba, General Abdul Salamu shine ya tsaya kai da fata kan Al'amarin Sadam! a cewar sa a wannan zamanin idan Najeria ta samu jajurtaccen mutum irin Sadam! zata samu cigaba irin wanda ake bukata. To tun Alhaji Auwal da Hjy Fatsima basa son abun suka dawo suna so domin General Abdu salam da kansa yazo ya sake wayar musu da kai kan yanda al'amarin suke sai suma daga baya suka gane abinda yake nufi. A da Sadam! yana karantar aikin likita ne wato bangaran mata to sauyawar ra'ayi yasa ya aje karatun likitanci ya shiga aikin soja gadan! gadan! A yanzu Sadam! nada mu'kamin Captain a brecck din nasu kuma suna masifar ji dashi saboda babu wani abu da zai tun karo su na tashin hankali bai magance musu ba, **** *Waiwaye adon tafiya* Wannan magana da Baba Ladidi da Baba Marka suke ta samo asali ne daga gurin marigayiya Baba Indo wato mahaifiyar sayyada kenan Baba Indo in dai baku manta ba 'yace ga Baba Ladidi ta kasance 'kanwar Alhaji Auwal da Kuma Kawu Tanko....To a tun lokacin da aka kaita dakin mijinta ta had'u da lalura wani ciwo ya fito mata a kafarta guda inda ya dinga cin jikinta a lokacin har ta haifi Sayyada tayi wayo kusan shekararta hudu a duniya saboda yanayin jinyar da Indo take ne yasa Baba Ladi ta dauketa ta koma gurinta da zama. To duk a wannan lokacin Ciwon ajali ya kwantar da Malam Jauro inda baiyi wata doguwar jinya ba Allah ya amshi ransa......Wata uku a tsakani Baba Indo ta bishi a ranar da zata rasu a ranar Sadam! yazo garin hutu.....Lokacin Sayyada tayi bud'ud'u da jar 'kasa hancinta dagaje! dagaje! da majina gashi lokacin kunnenta babu yari ga aski baba ladidi tayi mata saboda kuraje da suka dame ta Sayyada dai kwandala ba zaka siye ta ba, aikuwa rankwashinta yayi ta yayi mata tsawa! ya korata gida tana ihu! ta shiga gidan bayan baba ladi ta boya tana nuna shi shi kuma sai hararata yake....Baba Ladidi tace"Daga zuwanka zaka dinga dukanta wannan ai cin zaline da mugunta. Yana ya mutsa fuska yace."Baba wannan yarinyar sadaka aka bawa mutum ba zai kar'ba ba yarinya kamar ba mutum ba dubi jikinta ka'zama babu kyan gani." Tace."Ai wasa take kuma yanzu dama nake cewa bari nazo nayi mata wanka." Yace."Babu wani kawai don nayi magana ne amma da banzo ba haka zata kwana." Mikewa yayi yace."Zanje na duba Baba Indo kafin na dawo kiyi mata wanka." Cikin jin haushi Baba Tace"Ba zanyi ba d'in! kai kaji yaro da iyayi da kaine kake sani nayi mata wankan? sai dai idan ka dawo kayi mata ehee."! Fita yayi bai ce mata komai ba....Halin da ya iske Baba Indo a lokacin da ya isa gidan ya bashi tsoro Matan gidan sun kewaye ta suna mata fifita masu kuka nayi da salati baba indo kuwa bata san inda kanta yake ba sai nishi takeyi kamar ance ta bude ido sai ta ganshi a tsaye a kanta ta mika masa hannu matan gidan duk suka cika da mamaki hannunsa ta rike da kyau tana so tayi magana bakinta yayi mata nauyi da kyar tace"A kawo min Sayyada." Matar kanin mijinta ta fita daga dakin da sauri ta sanya yaro ya nufi can gidan ya fada musu halin da ake ciki......Minti ashirin ya kawo su Baba Marka ta fashe da kuka ganin halin da Indo ke ciki Ita kuwa Sayyada kin zuwa gurin mahaifiyar tata tayi ta 'buya a bayan Baba Ladi dake kukan zucci tana addua Allah ya saukakawa indo wannan larurar Mahaifin Sayyada ne ya shigo dakin tare da wani likita Ba tare da wani tunani ba likitan nan ya hada ruwan allura ya zurkuda mata a cewarsa allurar zata sanya ta samu saukin ciwon.....Ai ko minti biyar ba'ayi ba jiki ya rikice Indo ta dinga wata iriyar girgiza kumfa na fitowa daga bakinta sai a sannan kuma Bakinta ya bude ta dinga salati ta bude idanunta da suka jirkice tana kallonsu tana kiran sunansu tace"Sadam! ko bayan raina ina so ka auri Sayyada wannan shine burina Baba ku xama shaida na bawa Sadam! Sayyada Mahafin sayyada yace."Allah zai cika miki burinki Indo zaki samu sauki mu cigaba da rayuwa." Sadam! yace."Insha Allah baba kina raye zaki ga aurena da Sayyada nayi miki alkawai." tace"Mutuwa zanyi ku yafe min." Sai ta fara sha'kuwa tana salati a wannan lokaci Rai yayi halinsa. Wannan mutuwa tayi masifar girgiza zukatan mutane domin indo mutum ce mai shiga rai da barkwanci kowa sai da ya girgiza da jin mutuwar Indo Mussaman mutanan da suke rayuwa da ita a cikin gidan a wannan lokacin akayi mata suttura aka kaita gidanta na gaskiya, Sai bayan an dawo ne mutanan kaduna suka sauka a garin Alhaji Auwal yayi kuka sosai da mutuwar kanwarsa yana kaunar Indo shiyasa duk wani abun data bukata a lokacin tana raye a duniya yake mata......Sulaiman shima yaji mutuwar sosai tare suka dinga jajantawa junansu. Sulaiman na ganin Sayyada yaji wani tausayi da sonta a zuciyarsa duk girmanta haka yake daukar ta su fita yayi mata siyayyar cizi biskit alawa iri-iri Sayyada ta zauna tana shan abunta bata da wata damuwa saboda da kuruciya a tare da ita a lokacin. Sadam! kam ido ne nasa sam baya tanka musu watarana dai idan yaga abin yayi yawa sai ya daka mata tsawa idan tana wani shirman ita kuma sai ta fashe da kuka da ruga gurin Sulaiman tana fad'a masa shi kuma a lokacin ne zaka ga 'bacin ransa....Sadam! haushi da takaici ya sanya ya bar gurin sam a ganinsa abunda Sulaiman din yake wa yarinyar bai dace ba zata sangarce ta lalace duk girmanta sai ya dorata a cinya ko ya sa'bata a kafad'a ya fita da ita yana mata kiss a kumatu takaici kamar ya kashe shi.....Sai da sukayi fad'a kaca-kaca da Sulaiman din amma bai daina ba da karshe kawai sai ya daina kulashi gabad'aya to da yake Sulaiman din yafi shi saukin kai shine yake masa magana wani sa'in. Bayan sadakar bakwai suka shirya tafiya.....Sayyada ta dinga gursheken kuka kamar ranta zai fita Alhaji Auwal yace." A had'a kayanta xai tafi da ita Baba Ladidi tayi tsalle ta dire tace"Bata yarda ba....Sulaiman ya dinga lallabata har da yi mata alkawari zai kaita umara tace"In dai sai ta basu Sayyada zai kaita Umara to bata so. Sadam!!! 'bacin rai bai barshi yace komai ba shi dai ya zuba musu ido kawai sai da yaga iskancin Sayyadar yayi yawa sannan ya zare blet ya nufe ta yana zare ido......Ta ruga bayan Sulaiman tana kuka shi kuwa Sulaiman hararasa kawai yake yana fad'in"Wallahi ka dake ta da wannan blet din sai na rama mata mutum sai 'bakar zuciya kawai kai koma naka babu imani ka tausaya mata mana."! Tsaki! Yaja ya maida blet dinsa ya daura a gu'kunsa ya koma ya tsaya shaye da toka sai wani cin magani yake duk suna kallo Sulaiman din ya sa'bata a kafad'a ya fita da ita sunfi 'karfin rabin awa basu dawo ba Sadam!!! sai tsaki yake yana kallon agogo an kira wayarshi ya kai sau biyar ana jiransu a bracck dinsu akwai sabbin sojojin da zasu horar dasu. Mahaukaciyar siyayya Sulaiman yayi mata ta kayan zako iri iri Ya jibge baba ladidi ta cika da mamaki shi kuma yace."Ko idan sun kare ayi masa waya a sanar masa zai turo kudi." Baba Marka tace"Wannan ai ka siyo mata kayan ciwo haba ai abun yayi yawa za'ki ai ba abun sha bane." Yace."Baba komai Sayyada take so zanyi mata tausayi take bani." Tace."To dai banda irin wannan siyayyar ta cutarwa kasan halinta yanzu sai ta'ki cin abinci ta dimanci shan alawa da madara. Alhaji Auwal yace."Sai a kwashe kayan a dinga bata da kad'an-kad'an! Sadam!! yace."Nima dai abinda na gani kenan idan kun tara mata kayan za'ki taci ta sha to ku shirya da sanin cewar zata dame ku da kukan ciwon ciki."! *To wannan shine tushen labari* Page na gaba zamu dawo ainihin labari 30/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Free Pege 9 *Cigaban Labari* To haka Sayyada ta cigaba da rayuwa a hannun Baba Ladidi tare da kulawar 'bangarori daban daban mahaifinta ma yana iya bakin kokarinsa akanta sai da da yayi aure ne matar da ya aura ta janye masa hankali daga kan Sayyada ya daina kulawa da ita sosai Sayyada sam! bata sha'ku da bangaran mahaifinta ba tafi shakuwa da bangaran mahaifiyar ta shiyasa ba sosai take zuwa can gidan maigarin ba sai Baba Ladidi ta takura mata sannan take zuwa Juma'a Juma'a, shima idan taje bata wani zaman arziki take dawowa gida a cewarta baza ta zauna Hansatu tana yi mata kallon banza ba domin sun sha fad'a sosai da ita da matar baban nata mai suna Hansatu. Sayyada yanzu haka tana aji shida a karamar makaranta suna dab da jarrabawa makarantar isilamiyya kuwa sun hada izifi ashirin to babu laifi tana gane karatu amma Amina ta fita kokari, kun san dai kowa da irin baiwar da Allah yayi masa. ***** Karfe uku shaura na rana tana zaune da kwanon abinci a gabanta hijab ne a jikinta kalar ruwan toka gefanta jakar makarantar isilamiyya ce Amina ce tayi sallama ta shigo Ta gaishe da baba Ladi dake bakin rijiya tana wanke kwanoni kai tsaye ciki ta shige itama ta shirya tsaf da shirin tafiya makaranta. "Sayyada baki gama cin abincin ba kenan? duba lokaci ya kure da yawa kin san dai yau malam Bashir ne zai shigo ajinmu ko."? " Yi tafiyar ki malama kar ki dame ni! sai me idan malam Bashir ne zai shigo sai a ka fad'a miki tsoronsa nake."! Amina jikinta yayi sanyi tace"Kin san dai ko zai barki ki kishiga aji sai ya doke ki da wannan bulalar mai zafi shine abinda nake guje mana." "To me ya dame ki? kinga nifa bance dole sai na tafi dake ba tafiyar ki daban tawa daban mtwss! Baba Marka ta daga labule ta fito tana fad'in" Surutun me nake ji Amina."!? Amina data sha'ka da yawa tace"Baba Wai daga nace mata tazo mu tafi makaranta kar mu makara shine take fad'a min magana." Baba Marka tace"To bakya ganin abinci take ci ne." Amina tace"Ai dama cewa nayi tayi sauri baba." Marka tace"Ke Sayyada maxa ki gama ku tafi karku makara." Sayyada tayi musu shiru tana cin abincinta haushin Amina takeji sosai kuma tayi al'kawarin sai ta kunyata a gaban 'kawayensu na makaranta. Tana gama cin abincin ta mike ta wanke hannunta jakarta ta dauka ba tare tace Amina komai ba ta kama hanyar fita....Amina tabi bayanta tana fadin"Sai mu dawo." Baba Ladidi tace"To Allah ya bada sa'a." Ko a hanya ma Sayyada 'kin kula Amina tayi har suka isa makaranta Sayyada ta tsallake can gurin 'kawayenta itama Amina ta zauna gurin 'kawayenta dama gurin zaman Amina a gaba yake ita kuma Sayyada can baya take zama tare da manyan 'yan matan da suka girme ta nesa ba kusa ba suyi ta zancan aure sam basa gane karatu sai maganar aure da hirar samari Sai lokacin jarrabawa yayi idonsu ya raina fata Sayyada ce kawai mai 'kokarin cikinsu ita ke basu amsa ko kuma idan ta rubuta ta basu su kwafa shiyasa suke tsoronta komai tace dai-dai ne." Sai bayan malam bashir ya fita ne kafin wani malamin ya shigo Sayyada ta kallesu tace "Kun san menene."!? Suka ce sai ki fad'a." Tace"Wallahi na tsani Amina muguwar munafuka ce." Sadiya tace"Ke Sayyada ke da 'yar uwarki kuma me tayi miki."? Tace"Humm! wai saurayina ko kuma nace mijin da zan aura shi take so har da wani shishshige masa shi kuma har da sa mata zobe bayan fa tasan da al'kawari a tsakaninmu dashi." Ummi tace"Lallai Amina bata da kunya wallahi to ke wane mataki kika dauka."!? Sayyada tace"Ku taso muje inda take." babu musu suka mike suka isa inda Amina ke zaune da kawayenta suna bitar karatu. Aminta taji magana a kanta "Ke Amina ciro wannan zoben dake hannunki."! Sayyada ce me wannan maganar tasha kunu. Amina ta dago kai tana kallonsu tace" Kamar Yaya na ciro zobe me ya shafeki dashi." Ummi tace"Lallai Amina baki da kunya au! tambayar ta ma kike meye ruwanta bayan kinsan zoben hannun Saurayinta ne ai tana da iko dashi." Amina ta mayar da kai kasa tana karatu Sadiya tace"Wallahi tun muna shaida juna dake ki ciro mata zobenta ai itace tafi dacewa dashi tunda ita zai aura amma saboda tsabar shishshigi kin wani shigewa saurayinta wai don ya aure ki mun gane abinda kike nufi." Daya daga cikin kawayen Amina tace"A gaskiya wannan abinda kukeyi bai dace ba ina ruwanku da Amina ni dai tunda na shigo banga ta shiga sabgarku ba." "Dallah malama rufe mana baki banza 'kazama wacce bata waye ba ke idan ke akaiwa haka zakiji dadi? Mijina fa taje tana cusa kanta a gurinsa har sai da ya sa mata zoben da yayi niyar saka min wallahi sai ta cire zoben nan ko kuma ta raina kanta."!Sayyada ce ke wannan maganar tana girgixa jiki....Ai kafin kice komai 'yan ajin sun lullu'be su suna son jin 'karin bayani ita kuwa Ummi 'kawar Sayyada sai fad'a musu take Amina munafukace me 'kwacen saurayi don haka kowa yayi taka tsantsar da saurayinsa.......Aikuwa sai aka fara surutai kowa na fad'in albarkacin bakinsa. Amina 'bakin ciki ya sanya ta fashe da kuka idanu jage-jage da hawaye take kallon Sayyada tace" Yanzu ni kika tozarta a bainar jama'a Sayyada nifa 'yar uwarki ce."! "Oho! wannan ke ya shafa ni dai nace a ciro min zobe ko kuma yanzu jiki yayi tsami wallahi."! Amina tace" Wallahi bazan cire zoben nan ba tunda ai bake kika saka min ba sai ki bari idan wanda ya saka min zoben yazo sai ki saka shi ya cire min da kansa." Sayyada tayi wani juyi had'e da buga tsalle! sai ta cafki wuyan Amina ta sha'ke cikin hijab tana fad'in"Wallahi sai kin cire min zobe banza shashasha me 'kawacen saurayi." Amina da Sayyada kokawa suke sosai da sosai Sayyada duk ta ya kushe mata fuska sai 'kwa'kule mata hannu take tana murd'ewa wai dole sai ta cire zoben ita kuma Amina ta dunkule hannunta. 'Yan aji kuwa sai Ihu! suke suna dariya da fad'in"Wallahi babu wanda zai rabaku ku casu ai 'yan gida d'aya ne." Mariya 'kawar Amina ita ce ta nufi ofis d'in malamai domin ta fad'a musu halin da ake ciki sai suka ci karo da Malam Bashir ya fito daga ofis yana kokarin shiga wani aji tace"Malam Bashir ana fad'a a ajinmu.'' Yace."Waye da waye."!? Tace"Amina ne da Sayyada. Kai tsaye a jin ya nufa da zabgegiyar bulalar sa. Har yanzu kokawar suke Sayyada ta kusa ciro zoben Taji saukar bulala a bayanta ko a jikinta sai da ta ciro zoben sannan hankalinta ya kwanta ta saki wuyan Amina tana nishi! Amina ta mike zaune sai kuka take ga Sayyada duk ta ji mata ciwo da yakushi.....Malam Bashir yace."Ku same ni a ofis." Yana fita Sayyada ta mi'kawa Ummi zoben tace"Ri'ke min wallahi komai za'ayi ba zan bayar ba." Ta kama hanyar fita Amina ta mike da jiki a sanyaye tabi bayanta duk 'yan ajin suka bita da kallo Amina ta tsargi kanta sai rufe fuska takeyi kamar wacce tayi abun kunya. Suna isa ofis din suka tarar da Malam Bashiri na zaune kan kujera da wayarsa a hannunsa yace."Ku tsuguna ko wacce ta d'aga hannu sama." Babu musu sukayi abinda ya saka su sai da sukayi minti goma shabiyar a haka sannan yace."Ku sauke hannunku." Suka sauke Sayyada ya kalla yace."Daka gani kece mara gaskiya bari na fara jin ta bakin ki me ya had'aku fad'a."!? Sayyada ta soma inda inda" Malam nifa d dama ita k.....A gida bama shiri da juna kuma munafuka ce ita." Malm Bashir yace."Ni ba wannan na tambaye ki ba ina so ki fad'a min ma'kasudin fad'anku." Shiru tayi ya girgiza kai yace."Ko anan ma alamu sun nuna kece mara gaskiya Sayyada nagaji da halin ki yanzu yanzu zan kira Sadam! a waya in sanar masa da abinda kikeyi a makarantar nan." Sayyada gabanta ya yanke ya fad'i jin abinda yace sai tace"Nifa malam wallahi ba laifina bane itace ta shiga gona ta." Malam Bashir ya kalli Amina yace."Amina ke fada min abinda ya hadaku fada kafin na yanke hukunci." Amina ta warwarewa Malam Bashir duk abinda ya faru tsakaninta da Sadam! da yanda akayi yasa sanya mata zoben hannunsa. Malam Bashir yace."Sayyada kece mara gaskiya don haka a kanki zan dauki mataki ina ruwanki da zoben hannunta tunda dai ba ke kika saka mata ba ko kuma ance miki shi Sadam! din idan ya aure ki dake kad'ai zai zauna to ki shiga hankalin ki wallahi."Sayyada ta kama 'kunkuni hawaye na kokarin zubo mata....Malam Bashir ya fara neman numbar wayar Sadam sai da ya kira sau uku sannan ya dauka hands free ya bude duk suna jin muryarsa suka gaisa da malam bashir din wanda dama tun asali sun san juna abokan juna ne saboda duk lokacin da Sadam! din ya shigo garin a majalisarsu yake zama. Mlm Bashir ya fad'a masa dukanin abinda ke faruwa tare da fad'a masa hukumcin da ya yanke a kan Sayyada zai korata gida ta zauna sai bayan sati biyu ta dawo." Sadam! Yace."Yanzu ina Sayyadar take."? Malam bashir yace."Duk gasunan a kusa dani." Yace."okey bata wayar zanyi magana da ita." Sayyada najin haka sai gabanta ya fad'i! da sauri ta aro dauriya da jarumta ta kar'bi wayar da malam Bashir din ke mi'ka mata. _Afuwa bani da change sosai kuyi manege_ 31/5/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Free Pege 10 Dakakkiyar muryarsa mai cike da amo taji yana fad'in"Ina Sayyada."!? Baki na rawa tace"Gani." Yace."Wai ke me yake damun kwakwalwar ki ne? don Ubanki! ni da kaina kinji nace zan aure ki da har kike tozarta 'yar uwarki a kaina! ni me zanci dake ai idan aure zanyi Aminar zan aura tunda tafi ki komai da komai.....Tayi saurin katse shi ta hanyar fad'in"Ni wallahi Amina bata fini komai da komai ba."! Yace."Ni nake magana kina katseni wato nima zakiyi min rashin kunyar ko."? Shiru tayi bacin rai da bakin ciki yayi mata yawa, yace."Tun muna shaida juna dake ki cire zobe nan ki bata ai ina sane dake ban baki ba saboda ba ki dace dashi ba sai ita kuma wallahi kinji na rantse kada wata magana ta sake biyo bayan wannan a tsakanin ki da Amina idan kika kuskura nazo garin akace ga wani abu da kika sakeyi makamancin wannan to dama kin san sauran sai jikin ki ya fad'a miki kinji ko baki ji ba."!? Ba tare da ta amsa ba masa ta kashe wayar....Cike da mamaki! ya bi wayarsa da kallo wato yarinyar shi ta kashewa waya ashe haukan banza yake ba sauraransa take ba lallai Sayyada wuyanta ya isa yanka. Kiran wayar ya sake yi sai tayi saurin mi'kawa Malam Bashir wayar ya dauka tana jin sanda yake cewa malam Bashir din duk sanda ta sakeyin wani abu ya sanar dashi zai zo da kansa ya dauki mataki a kanta. Sukayi sallama da juna malam bashir ya kashe wayar sannan ya Umarci Sayyada da ta mayar wa da Amina zobenta tana zum'bura baki tace"Zoben baya hannunta tunda ta cire a cikin aji ta neme shi ta rasa. Malam Bashir dai yasan karya take saboda kar yaja maganar tayi tsaho yasa yace su koma aji Sayyada ta duba ko ina mutukar bata ga zoben nan ba to sai ya zaneta. To koda suka koma aji bata sauya zani ba don Sayyada habaici ta dinga yiwa Amina tana fad'in "Duk abunda xa'ayi sai dai ayi amma ba xata bada zobe ba. Ita dai Amina bata ce mata komai ba ta zauna cikin kawayen ta kunya duk ta isheta ganin irin kallon da wasu suke mata. ***** To haka suka cigaba da rayuwa tsakanin Sayyada da Amina babu jituwa kullum fad'a kuma Sayyadar ce ke takalo fad'an har ta kai ta kawo suka daina kula junansu saboda Sadam! wanda shi da suke abun dominsa ma bai san sunayi ba. " Oyoyo Yayana" Oyoyo sannu da zuwa." Sayyada ke wannan ihun tana tsalle tun sanda taji Sallamar Sulaiman a 'kofar su da gudu taje ta rike hannunsa shi kuma ya dan rungume kafad'anta fuskarsa dauke da murmushi wanda ya kara masa kyau da kwarjini yana mata wani irin kallo yace."Babyna kece kika girma haka.'"! Cikin kunya ta rufe fuskarta tana kokarin kar'bar jakar kayansa....Murmushi ya saki yana d'an shafa siririn sajen sa yace."Masha Allah babu shakka Baba Ladi ta iya raino akwai gwaggwa'bar kyautar da zanyi mata." Baba Marka ta d'aga labule ta fito daga d'aki tana fad'in"Murya wa nake ji ne kamar ta soja." Da Sulaiman tayi tozali tace."Au! ashe bature ne to sannu da zuwa lallai yau za'ayi ruwa da 'kankara *Dabi* tana da babban 'bako." Sulaiman yace."Kwarai kuwa baba yau naso nayi suprise d'in ku ne shiyasa kawai kuka gani ba tare da kunyi tsammani ba." Baba Marka na shimfid'a masa sabuwar tabarma tace"Aikuwa dai munyi mamaki kwarai da alama ma zaka kwana biyu a garin tunda na ganka har da guzirin kaya." Yace."Zanyi sati biyu insha Allahu kafin in koma, wai ina d'aya matar tawa ne."!? Yana nufin Baba Ladidi Sayyada tace"Yanzu yanzu ta tafi sabuwar kasuwa, amma dai nasan yanzu zata dawo." Yace."Okey. Baba Marka tace"Bari in dama maka fura kafin a d'ora abinci." Yace."Nagode Baba sosai nayi kewar wannan furar taku mai dad'in gaske." tana dariya ta mike ta shiga daki....Sulaiman ya tsirawa Sayyada ido yana kallonta sosai yake masifar son yarinyar a cikin ranshi yana ganin idan da babu maganar aure a tsakaninta da 'kaninsa da babu abinda zai hanashi auranta sonta ya riga ya zama jinin jikinsa. Rife fuskar ta tayi tana murmushi tace"Wayyo Yayana wai na sauya maka ne naga sai kallona kake tun da kazo." Ya saki murmushi mai kyatarwa yace."Sosai kika sauya min Sayyada kin girma kin zama cikakkiyar mace alhamdullahi ina rokon Ubangiji ya baki miji nagari wanda zai kula dake." Murmushi kawai tayi tace "Yayana ina auntyna." Yace."Tana nan lafiya lau da da tare zamu zo to saboda yanayin jikinta ne ya sanya nace ta bari sai ta haihu sai na kawo ta ta kwana biyu tare daku." "Wayyo Allah ashe auny Luba ta kusa haihuwa kai gaskiya naji dad'i wallahi Allah ya sauke ta lafiya." Yace."Ameeen ya rabbi Sayyada ya karatu ina fatan kina mai da hankali ko." ? Tace"Eh Munayi yayana A dai taya mu da addua."Yace."Idan kina so in tafi dake can kaduna mana sai ki cigaba da karatun ki a can ni sai nake gani kamar bakya mai da hankali anan." Jiki a sanyaye tace"Wallahi ina karatu Sosai Sai dai kasan makarantun cikin birni da irin namu ba d'aya bane amma nima ina ganewa sosai." Yace."Okey zanzu kuna jiran jarrabawa ta fito kenan." Tace"Eh kuma isilamiyya ma mun had'a izifi ar'bain." Yace."Alhamdullahi to kafin in koma za muyi karatu ni dake sai in gani shin da gaske kike kina fahinta ko kuwa." dariya tasa tace"Tom ai kuwa zan baka mamaki."! Mikewa tayi tace"To bari dai in dora maka abinci ko." murmushi yayi ya bita da kallo yana ayyana abubuwa da dama a kanta. Baba Ladidi ta shigo da daurin buhu a hannunta wani a kanta tana ganinsa a ki shingide ta saki fuska da fara'a ta karaso tana fad'in"Ashe bature ne a gidan namu sannu da zuwa ai jikina yayi ta bani dama zanyi babban bako." mikewa yayi zaune yana mata sannu da zuwa tare da bin buhuhunan da take ajiyewa da kallo. Mayafin dake saman kanta ta cire ta rataye a giya tace"Sayyada kawo min ruwa nasha kafin mu gaisa da mai gidan nawa." Sayyada ta mika mata ruwa cikin kofi da ta d'ebo a randa Baba Ladidi ta shanye ruwan tas ta aje kofin kafin kice kwabo gumi ya yanke mata sai ta fara neman mafici Sayyada ce ta mika mata ta hau fiffita tana fad'in"Kai nasha rana wallahi ai da yake yau juma'a shine kowa ya fito ya ci kasuwarsa amma ai bukata ta biya tunda na samo abinda nake so."! Yace."Wai Baba daga ina kike haka kin dauko rana gaki dauke da buhuna sai kace wacce zata bar gari." Baba Ladi ta gyara zama tare da jawo buhun da ta shigo dashi tana fad'in"Naje na d'an yo sare-saren kayan siye da sayarwa kasan zama babu sana'a babu dad'i ko yaya kana d'an motsawa sai kaga asirin ka ya rufu." Yace."Idan na fahinta kina so kice asirin ki a tone yake yanzu."!? Tace."Oo!! ni ban fad'a ba ni nace asiri na a tone yake ai idan nayi haka nayi wa Allah butulci.'' Yace"To meye kuma zaki dinga d'aukar rana kina shiga kasuwa salon ki jawo mana zagi menene ba a siya muku na abinda kuka bukata."? Tace"Sulaiman rabu dani don Allah nifa ba zan zauna haka kawai na rungume hannuna ba bana sana'a kawai sai in dogara da wani kuje ku ri'ke abunku ni ku barni na nemi kud'i na." Girgiza kai yayi yace."Ai kaji irinta ita baba Marka me yasa bata sana'ar sai ke ? ke dai kawai kice kina da son kudin tsiya kuma haka zaki tara mana ki tafi ki bari." Tace"Eh ai haka yafi akan in mutu mutanan gari na fad'in ban bar muku komai ba. Sai dai duk abinda zakuyi kuyi sana'a kam yanzu na fara wancan miskilin ma da ya fika 'bakar zuciya yayi ya gama kuma ya hakura ya kyaleni bare kuma kai."! Dariya ya sanya yace."To ai shikkenan Baba kiyi sana'a Allah ya bada sa'a." Tace"Ameen." Baba Marka ce ta fito daga daki dauke da kwanon sha ta damo fura tayi luwai taji nono mai kyau ta aje gabansa yace."Ina godiya Baba gyara zamansa yayi ya sanya ludayi ya fara shan furar cikin nutsuwa. Baba marka tace"Ashe kin dawo to ya kasuwar yau dai da alama babu cikowar jama'a naga kin dawo da wuri." Baba Ladi tace"Aikam akwai cinkoso Allah ne kawai yasa zan dawo da wuri na samo mangwaro masu kyau da za'ki irin wanda yara suke so." Baba Marka tace"Aikuwa yanzu xaki ga ya 'kare yara da son mangwaro." Baba Ladi ta zazzage buhun mangwaron tace"Kinga irinsu so."!? Da sauri Sayyada tazo gurin tana fad'in"Gaskiya baba mangwaron nan zaiyi za'ki."! Baba Ladi tace"Maza jeki dauki wannan katon farantin ki kasa mangwaron a ciki kije can bakin darbejiya ki zauna wannan mangwaron ba yara kad'ai ba har da manya sai sun siya saboda yana da 'kwari." Baba Marka tace"Aikuwa dai gaskiya yau kinyi sa'ar zuwa." Sayyada ta dauko katon faranti ta shiga jera mangwaro akai Baba Ladidi tace"Guda daya naira goma shida hamsin." Sayyada tace"To fara bani nawa in sha tukkuna."Tace"Kije ki dawo gashi na ajiye miki masu za'ki." hijab din ta ta zara ta zura ta dauki katon farantin dake ciki da mangwaro zata fita Sulaiman yace"Ke Sayyada dawo da kayan tallan nan." Sai taja ta tsaya ganin fuskarsa a hade yasa jikinta yayi sanyi sam bata son taga yana fushi da ita sai ta dawo ta zauna....Ita kuma Baba Ladidi ta hau zazzaga masifa kan bai isa daga zuwansa ya hanata abinda takeyi ba har da cewa Ubansa ma yayi kadan bashi ba, shi dai sulaiman baice mata komai saboda yasan halin jarabar ta bayan ya ci abinci ne sai da ya tabbatar Sayyadar ta tafi isilamiyya sannan ya fita daga gidan kai tsaye gona ya nufa inda Kawu Tanko yake....! Sosai ya nuna masa 'bacin ransa kan ya akayi suka sake har Baba ke fita cikin kasuwa tana sare sare sai kace wacce ta rasa ci da sha sannan babban abin damuwar yanda take dorawa Sayyada tallah wannan ai zubar da mutumnci ne, Kawu Tanko yace"Shima ba a son ransa hakan take faruwa ba Baba dai mahaifiyar sa ce dole yayi mata biyayya amma yana ganin wannan karon dole yayi ta maza tunda dai abin nata na kokarin wuce gona da iri sannan maganar tallan da take d'orawa Sayyada kuwa zai sanar da ita cewar zai je ya shaidawa iyayenta tunda dai su basu suke da iko da ita ba yasan can gidan maigarin basu san abinda ke faruwa da tuni sun dauki mataki kan al'amarin domin kankaro da martabarsu tabbas ya fada mata haka yasan zata daina dora mata tallah tinda itama bata so mutuncin ta ya zube a gurin mutane. Sulaiman yace"Wannan hukuncin da ka yanke shine ya dace tuntuni a dauka a kanta.....Sai daf da magariba suka nufo gida a tare abin mamaki suna dosowa layin suka hango Sayyada gindin darbejiya tana sai da mangwaro Talle na zaune a gefanta sai hira suke...Kawu Tanko yace."Ka gani ko Sulaiman duba ka gani." Sulaiman ya kalli inda yake nuna masa hankalinsa ya tashi ainun kai tsaye gurin ya nufa ransa a 'bace! Talle na ganin ingarmar namiji ya doso gurin sai yayi sauri ya mike duk a tunaninsa ko Sadam! ne domin bai manta da marin da yayi masa a watannin baya sai da Sulaiman ya karaso gurin sannan ya gane bashi bane domin shi wancan yafi wannan fad'i da murd'ewar jiki sannan bai kai hasken wannan ba amma dai duk da haka dole ya kiyaye domin ya lura shima wannan d'in babu sauk'i a fuskarsa.Gurin yayi saurin bari Sayyada na kwala masa kira yazo ya 'karbi sanjinsa yace."Ki rike na bar miki." Tace"To nagode." Sulaiman yace"Sayyada ashe kema baki da kamun kai ashe baki san ciwon kanki ba Sayyada! bayan fitata ashe dai sai da kika d'auko tallan mangwaro kika fito bakin bishiya shin wai me kuke nema ne ke da Baba Ladidi? babu rashin ci babu rashin sha babu rashin suttura kuke nema ku zubar mana da mutunci a gari dai dai gwargwado muna sauke hakkinku banji dadin abinda kikeyi ba shin wannan saurayin da yake zaune a kusa dake meye matsayinsa a gurinki.'!? Tana kuka tace"Saurayina ne Talle." Sai yaji gabansa ya fad'i! Yace."Saurayin ki ne Talle ."!? Daga kai tayi girgixa kansa yayi yace."Dauko kayan muje gida." Ta sunkuya ta dauki farantin mangwaron suka nufi gida Sulaiman takaici na cin zuciyarsa dole tilas kafin ya bar garinan ayi wacce za'ayi Dole ne Sadam! yayi wani abu akan lamarin nan sam! shirun da yayi bashi da wani amfani kawai ya fad'i abinda yake ransa shin yana son yarinyar nan ko baya so idan baya so to babu shakka shi kam kafin ya koma bakin aiki sai ya tabbatar da cewar an d'aura masa aure da ita ya tafi da matarsa inda yake da wannan tunanin suka isa gidan Kawu Tanko na tsugune gabanta yana magana 'kasa-'kasa da son ya fahintar da ita cewar abinda takeyi ba dai-dai bane ita kuma sai furjewa takeyi tana kawo 'kauli da ba'adi! Sulaiman najin tababar da suke yace."To shikkenan tinda kin'ki fahinta mu zamu shigar da 'korafin mu gaban maigari in yaso sai ki fad'a musu dalilin da ya sanya kike d'orawa 'yarsu tallah."! Ai sai ta fashe da kuka tana fad'in Sulaiman bashi da kunya yana kokarin zaginta ya fad'a mata magana in dai kan Sayyada suke wannan maganar to ta zare hannunta daga kanta. Sulaiman yace."Shikkenan kin gama magana tace"Ban gama magana ba ai tunda kunce Sayyada ba zata yi min tallah ba to sai ku sanar da wancan miskilin mai kafirar kafiyar tsiya ya fito a daura auran in daina ganinta a gabana idan kuma ya'ki to wallahi nima ba zan daina d'ora mata tallah ba." Sulaiman yace"In dai wannan ne babu matsala ni da kaina yanzu zan kirashi a waya mu gama magana nima nagaji idan yana so ayi dashi idan baya so sai ya barwa masu so ko ba haka ba Kawu."!? Kawu Tanko yace."Kwarai kuwa maganar nan itace gaskiya amma ka fara sanar da mahaifinka halin da ake ciki idan da hali ma yazo sai ayi maganar shima Sadam! din yazo a taru guri guda a tsayar da maganar." Baba Marka tace"Wannan itace shawara mai kyau." Sayyada kam d'aki ta shige ta dauki pilo ta rungume tana lumshe ido hakika tana son Yaya Sadam! taji dadi kuma da manya suka shiga cikin maganar dole ko ya'ki ko yaso ya aure ta tinda manya sun sanya baki yanzu Allah Allah take yazo garin ayi wacce za'ayi. Sulaiman na shiga masaukinsa ya fara neman numbar wayar Sadam!! Sai da ya kira sau kusan hudu bai dauka ba sai ana biyar d'in sannan ya dauka gaisawa sukayi babu yabo babu fallasa domin dama can babu wata kyakkyawar jituwa a tsakaninsu....Sulaiman yace."Tuntuni nake kiran wayarka ka'ki dauka saboda wulakanci ko."!? Sadam! ya dafe kansa cikin 'kosawa yace."Shikkenan mutum bashi da wani uziri a rayuwarsa lokacin da ka kira wayar nan ina tare da mutane ne kai ka fiye 'korafi wallahi."! Yace."Okey ba wani abu bane dama Kan maganar Sayyada ne yanzu haka ina cikin *Dabi* kuma duk naga abinda ke faruwa da Sayyada shin wai kai a wace matsayar ka tsaya ne kan al'kawarin daka d'auka a kanta." Ransa ya d'an 'baci da jin abinda d'an uwan nasa yake fad'a yace."Ban gane abinda kake nufi ba."!? Sulaiman yace."Ina nufin ya maganar auranka da Sayyada zaka aure ta ko yaya? muna so muji magana guda daga bakinka." Kai tsaye! yace."Ba zan aure ta ba."!!! Sulaiman yaji wani iri a jikinsa....Yace."Ko zaka fad'a min dalili."? "Bani da lokacin wannan magana a yanzu akwai aiki a gabana."! Sai ya kawai ya kashe wayar takaici ya cika zuciyar Sulaiman Sadam! zai aikata abinda ya fi haka yanzu dai dole ya sanar da mahaifinsu halin da ake ciki a waya ya kira shi ya sanar masa da abinda ke faruwa Alhaji Auwal yace." Insha Allahu zai shigo garin domin ayi magana d'aya saboda shima al'amarin ya soma damunsa kuma dole ne Sadam! d'in yazo shima ayi zaman dashi kowa yaji ta bakinsa. Da wannan maganar sukayi sallama da juna. Da 'kyar! Alhaji Auwal ya shawo kansa kan cewar ya iske su a can *Dabin* da da farko yayi ta kawo Uzirirrika Alhaji Auwal yace"Duk wani Uzuri da yake dashi tilas ya aje yaje Kiran da ake masa ba yanda ya iya tilas ya shirya tsaf ya nufi garin Jigawa cikin 'kauyen *Dabi* **** Sayyada najin ance yazo ta fito daga daki ta cika bokiti da ruwa a gurguje tayi wanka ta fito sabuwar atamfar ta tasa ta gyara dogon gashinta sosai sai kyalli yake daurin dankwali tayi mai kyayatarwa ta fesa turare mai sauki kamshi idan ka kalleta ba zakace a kauye take ba saboda tana da d'an waye wa ba kamar Amina ba Sayyada na 'kawance da 'yan matan da suka girmeta shiyasa tasan komai na fanni aure domin idan sun zauna yasu yasu basu da wani zance sai na aure da yanda ake rayuwar aure. Sadam! bai wani samu tar'bar arziki ba kowa haushinsa yake ji yaga duk suna binsa da kallo kamar wanda yaci bashi zama yayi gefan dan uwansa ya mika masa hannu suka gaisa sannan ya gaishe da iyayen nasa da kakanin nasa, Baba Marka tace"Bari ka fara cin abinci tukkuna sai komai ya biyo baya." Abinci taje ta kawo masa da ruwan randa mai sanyi ta aje a gabansa ganin towon shinkafa ne da miyar taushe yasa ya zage cikinsa yaci ya sha ruwa sannan ya kauda kayan abincin dake gabansa guri ya nutsu Alhaji Auwal yace."Abinda yasa kaga mun taso ka daga gurin aikinka da gaggawa magana ce mai muhimanci kuma wannan maganar itace karshen magana a tsakaninmu da kai insha Allah, maganar ba wata sabuwa bace nasan idan kai mai fahinta ne zaka gane inda na dosa to amma dai yana da kyau mu sake fad'a maka shin dukaninmu anan muna so mu san inda maganar auranka da Sayyada ta kwana shin zaka aureta ko kuwa."? 1/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Free Pege 11 Shiru yayi tare da sunkuyar da kansa Alhaji Auwal yace."Da kai nake magana kaji abinda nace kuma ka sunkuyar da kanka 'kasa, shin ya maganar auranka da Sayyada."!? Ya kara maimaita masa maganarsa ta farko. Ys dago kansa sam babu walwala a tare dashi yace."Abbah koma meye a tsakani na baku wu'ka da nama ni bani da ta cewa akan wannan al'amari." Baba Ladidi tace"Bamu gane wannan maganar taka ba so muke kayi mana bayani yanda zamu gane inda ka dosa ba kace ka bar mana komai a hannunmu hakan yana nufin ko auran aka daura itama Sayyadar zaka bar mana ita kenan." Yace."Iya abinda zan iya cewa kenan saboda nasan idan nace muku ga ra'ayi na ba zaku amince ba ni na hakura zan bi ra'ayin ku na amince da auran Sayyada." Baba Marka tace"To yanzu kayi magana mai ma'ana." Sayyada na bakin kofar daki a la'be taji lokacin da yace ya amince zai aureta sai ta ruga daki da gudu ta kwanta kan gadon karfe na Baba ta ringume pillo tare da lumshe ido tana murna da farin ciki itama zatayi aure taji abinda su Sakina sukeji kullum idan sukaje gidan kawarsu Sakina da akayi mata aure babu hirar da sukeyi sai ta aure Sakina tayi ta basu labarin yanda ake kwanciyar aure da dad'in da ake ji....Sayyada tayi ta mutsu mutsu a lokacin tun bata gane sha'awar namiji ba har ta gane domin duk lokacin da zasuje gidan Sakina suyi irin wannan hirar haka take wuni jikinta a sanyaye tayi ta shiga bandaki tana wanke gabanta.....Duk sanda ta tuno Sakina tace musu mijinta na tsotsar mata nono sai tayi ta mamaki! Sai ta dinga hango Sadam! itama nayi mata haka idan kuma ta kalli gallafirin nonon nata sai taji rashin dad'i domin a ganinta ba zai ta'ba cika masa hannu ba duk da ta girmi Amina ta fita nono sai dai kuma ita tafi Aminar fad'in 'kugu da d'amamman ciki tamkar wacce bata cin abinci.... Baba Ladidi ce ke ta rangwada bud'a tana fad'in"Alkawarin Allah ya cika babu shakka Sadam! baka ta'ba burgeni ba irin yau insha Allahu zakaji dad'in zama da Sayyada kai dai kawai abinda zance maka shine ka kyautata hakuri Allah ya sanya alkairi." Sulaiman kuwa tun sanda Sadam! din ya nuna amincewarsa kan auran ya kasa d'ago kansa so yake kawai ya dai-dai ta kansa sam baya so su fuskanci halin damuwar da yake ciki hakika zai sha fama da zuciyarsa mutukar Sayyada ta kufce masa....Hankici ya ciro ya goge gumin fuskarsa ya d'ago kansa suka had'a ido da d'an uwan nasa wanda yaso ya fuskanci wani abun amma kawai sai ya basar ya dauke kansa 'karshe ma tashi yayi ya bar gurin Sayyada na hango abinda ke faruwa a tsakar gidan tana ganin ya bar gurin ta fito tana 'boye fuska, Alhaji Auwal yace."Kunyata ake ji ne Sayyada."? Fuska a rufe ta gaishe shi taje bayan Baba Marka ta 'buya ranta fari tas tas Allah ya kusa cika mata burinta Amina kuma sai dai ta mutu da ba'kin ciki. **** Kwata-kwata Sadam! baiyi niyyar kwana ba a garin yaso kawai ya juya tunda ya gama abinda ya kawo shi dukaninsu suka nuna rashin amincewar tafiyarsa sai ya hakura kawai yabi ra'ayinsu ya bari sai da safe sannan ya dauki hanya.......Karfe goma sha d'aya saura na dare yayi sallama da majalisar su Bashir malamin su Sayyada kenan na isilamiyya kai tsaye gidan ya nufa....Shiru lokacin da shiga duk suna kwance a tsakar gida kasancewar lokacin zafi ne Baba Marka da Baba Ladidi da Sayyadar Alhaji Auwal kuwa da Sulaiman suna can 'bangaran Kawu Tanko can zasu kwana.....Hasken wayarsa ya kunna yana haskasu can ya hango Sayyada na motsi idanta biyu dama taji lokacin da ya shigo kunyar tashi take kasancewar rigar dake jikinta 'karama ce mai hannun shimi dake sam bata son zafi duk da ta kasance siririya sam bata kaunar zafi shiyasa idan zata kwanta take sanya karamar riga don tasha iska....Ganin tana motsine yasa yayi saurin dauke hasken wayarshi daga kanta ya nufi masaukinsa. Sayyada ta bishi da kallo tana lumshe ido....Yana shiga dakin ta mike da sauri ta shiga dakin Baba Ladi, Zani ta daura kan rigar baccin amma bata rufe kirjinta ba ko dankwali babu ta dauki tire din abinci da aka jera masa ta nufi dakinsa.....Yana tsaka da zage tazugen wandonsa ta shigo da sallama kasancewar dakin akawai duhu yasa ba taga komai ba shima nasa 'bangaran yaji dad'in hakan....Tsawa! ya daka mata "Malama me ya shigo dake d'akina da wannan lokacin." !? Tace"Baba ce tace kar nayi bacci har sai ka dawo na baka abinci sannan sai in kwanta." Ya dauki wayarsa ya kunna torchlight yana haskata gabansa ne ya fad'i ganin irin rigar dake jikinta ya dauke kansa da sauri yace."Me yasa ba aje min ba tunda dakin ai a bude yake ko dole ne sai kin bani da hannunki." Tace."To aini ma ba laifina bane." Tsaki yaja yace."Meye abincin."!? "Dafadukan shinkafa ce da busassan kifa." Shiru yayi na minti biyu ita kuma ta aje tiran kayan abincin zata fita yace."Dawo ki zuba min abincin sai ki tafi." Ta dawo da baya tana sanja tafiya wai ita dole ga budurwa sai ta janye hankalinsa. Ta sunkuya tana zuba masa abincin shi kuma yana haske ta da hasken wayarsa 'yan 'kanunun nonowanta yake hangowa daga cikin rigarta ya kura musu ido yana kallo hannunsa ya duba yaja tsaki! tayi saurin kallonsa harara ya watsa mata ta dauke kanta tana ta'be baki hannunta ya kurawa a ido yana kallo yace."Ke! wane zobe nake gani a hannunki."!? gabanta ya fad'i! sai tayi saurin 'boye hannun yace."Ina wasa dake kenan ba tambayar ki nake ba don Ubanki."! Cikin rawar baki tace"Zobena na ne."!? yace."A gidan Uban wa ya zama naki ashe dama bakijin magana ba cewa nayi ki mayarwa da Amina ba ashe baki mayar mata ba shin wai ke me kike so ki zama ne."!? Tace"To ai gani nayi zoben bai dace da ita ba shiy....."Rufe min baki anan gurin ko kuma yanzu in mareki wallahi! maza maza! ciro min zoben nan ko yanzu in 'ballaki."! Da sauri ta nufi hanyar fita....Ya mi'ke cikin zafin nama ya cafko tsintsiyar hannunta yana murd'ewa zubewa tayi nan bakin 'kofar ya sanya 'kafa ya tura 'kofar ta rufe gam!! d'aukar ta yayi kamar jaririya ya jefa ta kan katifar ta mike da sauri tana kallonsa, yace."Zaki ciro zoben nan ko kuwa zaki tsaya gaddama."! Shiru tayi tana motsa baki ya hayo kan katifar da sauri ta matsa yace."Dama na fad'a miki idan kinyi min laifi da abinda xan hukunta ki zaki Ubanki yanzu yanzu."! Sayyada shaf ta manta da irin hukuncin da zaiyi tace"Ni wallahi bazan ciro zoben nan ba tunda ina sonsa kuma dai naga an gama tsayar da magana a tsakaninmu da kai idan auran Aminar zakayi sai ka fad'a mu sani." Ko kallonta baiyi ba ya matse ta jikin bango yana me d'amkar brest dinta guda d'aya al'amarin yazo mata a bazata! ta bude baki zatayi ihu! ya rufe mata baki da tafin hannunsa. Jikinta ne yake ta kyarma! tsigar jikinta na tashi duk ta rasa yanda zatayi shi kuma sai mulmula mata Brest yake.!!! Sai da yaga tayi la'kwas! sannan ya bar abinda yake ya kama hannunta ya zare zoben murya a hard'e! yace."Tashi ki bawa mutane guri."! Simi! simi ta sauko ta dauki zaninta ta d'aura ta kama hanya ta fita. Tana fita ya sauke wata zazzafar ajiyar zuciya ya mai da zobensa hannunsa minti biyar a tsakani ya fito sanye da jallabiya bandaki ya nufa dole sai ya tsarkake jikinsa don wannan abin da yayi sai da yaji alamun fitar ruwa a tare dashi. Sayyada kam! bayan Baba Ladidi ta kwanta tana ta takure jikinta motsi kad'an sai tsigar jikinta ta mi'ke wani irin yanayi takeji a jikinta mara misali ga kan nononta duk ya kumburo sai kyaikyayi suke mata kuka ta farayi jin al'amarin yana so ya wuce gona da iri Yana fitowa daga bandaki ya ji shashshakar kukanta da sauri ya shige daki ya rufo kofa tare da jan dogon tsaki. Baba Ladidi ta farka tana kokarin mikewa zaune tace"Ke Sayyada kukan me kike da wannan daran." "Baba cikina ne ke ciwo."! tafada tana shashsheka...." Assha!! to ba sai ki tashi ki dauko kanwa ki kad'a ba sai kawai kiyi kuka." Baba ta fad'a a lokacin da take kunna fitila Sayyada ta mike da jiki a sanyaye ta dauko kanwa da ruwa a kofi ta kad'a tasha ta koma ta kwanta.....Baba Ladi kuwa zama tayi har sai da sayyadar tayi bacci sannan itama ta kwanta. *Asubah ta gari* Karfe bakwai ya fito a shirye da nufin tafiya nan duk ya gansu suna karyawa ya gaisa da kowa ya nemi gefe guda ya zauna fuska a daure Baba Marka tace"Ni dad'ina da kai kenan baka da fara'a wallahi kowa na cikin walwala da farin ciki kai kana d'aurewa."! Yace."Haka kawai sai na hau dariya kamar wani mahaukaci."! tace"Oo! ni ba haka nake nufi ai dai ka saki fuskarka tunda ka fito ka ganmu a zaune muna raha." Murmushi yayi sai yayi wani masifar kyau tabbas da ya san yanda murmushi ke masa kyau da ya dinga yi.....Baba Ladidi tace"To ko kaifa ai wannan zaman da mukayi duk naku ne kai da Sayyada muna shirya yanda al'amarin biki zai kasance domin mun riga mun tsayar da cewar sati hud'u kacal xa'a daura aure." Ya d'ago kai yana kallonta cike da d'umbin mamaki! Alhaji Auwal yace."Kwarai kuwa naga kamar kana mamaki! to wannan maganar ma ba daga gare mu ta fito ba daga can gidan maigari ne domin dai ka san sune suke da iko akanta da asubah bayan mun fito daga sallah can gidan maigarin muka nufa domin mu tsaida magana." Yace."To sai naga al'amarin kamar akwai cutawar wa a ciki maganar karatun ta kuma fa kada ku manta fa wannan shekarar ta gama 'karamar makaranta pramiry zata shiga secondary mai zai hana a bari ta kammala tukkuna nima kafin lokacin na samu nutsuwa." Alhaji Auwal yace."Maganar karatu ai mai sauki ce Sadam! ina gani ai zata iya cigaba a dakinta wannan ba matsala bace." Sulaiman yace." 'Kwarai kuwa." Wata harara ya watsa masa yace."Ni wannan ba ra'ayina bane Abbah kasan kowa da tsarinsa mutukar kuka d"aura min aure da Sayyada a irin wannan lokacin to gaskiyar magana shine ta gama karatu saboda bana da ra'ayin iyalina na cud'anya da maza da sunan karatu." Baba Ladidi tace"Wai shin karatun dole ne! jama'a! ku kyaleshi kawai ai yayi tsinkaye da hangen nesa kuma hakan ya nuna mana cewar yana kishin kansa da iyalinsa don haka maganar karatu a bar ta Allah ya amfana wanda ta samu." Sulaiman yaji wani irin takaici da 'bakin ciki ya turnukeshi yanzu yarinya 'kan'kanuwa kamar Sayyada za'a tauyewa rayuwa ayi mata aure da 'kananun shekaru sannan kuma saboda tsabar kin gaskiya da son kai a goyi bayan hanata karatu a dakinta wannan tauye hakki yayi yawa tabbas in da shine ya samu nasarar auran yarinyar sai ya gatanta ta ya barta tayi karatu mai amfani ta hau matsayin da duk wata mace mai matsayi take hawa Ya lura Sadam! ba wani son yarinyar yake ba kawai don dai sun tursashi ne zai aureta a wannan ga'bar bashi da tacewa sai dai kawai ya roki Allah kan abunda ke damun ransa. Alhaji Auwal bai so Mahaifiyarsa ta goyi bayan hakan ba to amma saboda yasan bashi da abinyi sai kawai yace."Dama ai karatu ga 'ya mace ba dole bane suturarta da mutuncinta shine dakin mijinta to shikkenan mun bar maganar Allah ya sanya alkairi." Sadam! da Alhji Auwal ne kawai suka tafi a ranar shi kuma Sulaiman yace sai ya kara sati guda tukkuna sannan zai koma. *** Sayyada kam murna kamar ta zuba ruwa a kasa tasha daga jin an tsayar da ranar daurin auransu da Sadam! ta dinga yiwa Amina habaici 'kawayenta kuwa babu wanda bai san zancan ba in sun zauna zancen kenan na aure suna koya mata abubuwa da yanda zata dinga yiwa mijinta kullum idan antashi daga makaranta sai su nufi gidan Mariya suyi ta zungurarta ita kuma tai ta fayyace musu yanda auran yake. Amina ta shiga wani irin mawucin halin lokacin da taji maganar auran Sayyada da Sadam! ya tabbata kullum sai tayi kukan bakin ciki duk ta tsargu da kanta gashi idan taje makaranta 'yan ajinsu suyi ta nunata suna mata dariya mai son wanda baya sonta da yake sunan da Sayyada take kiranta dashi kenan ganin zata halaka kanta ne yasa ta yanke shawarar duk lokacin Yaya Sadam! din yazo zata sanar masa da abinda Sayyadar take mata sannan zata roke shi ya had'asu ya auresu ko don ma'kiya suji kunya *Tofa shin wannan al'amarin zai yiwu kuwa? wai ma Sadam! na son Sayyada da gaske ko sha'awarta yake!? Meye matsayin Amina a zuciyar Sadam! Wane irin xama za'ayi tsakanin Sadam da Sayyada? Wane al'amari ne zai faru anan gaba!?* _Muje Zuwa_ 2/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ Pege 12 Gaba mai tsanani ce ta shiga tsakanin Sayyada da Amina ta inda har sai da tsofaffinsu su gane basa kula juna wanda da can baya suke mutukar shiri da junansu duk inda kaga Sayyada to zaka ga Amina a gurin tare suke cin abinci su tafi makaranta tare komai nasu tare sukeyi amma tunda al'amarin auran ya tabbata shikkenan suka raba gari wanda inda ta Amina ne zasu iya cigaba da mu'amularsu to kullum taje makaranta 'kawayenta sai sun zugata sunce kar ta sake sakin jikinta da Amina xata shiga tsakaninta da masoyinta wannan dalili ya sanya Sayyada sake nuka wulakancin da take wa Amina yafi na da yawa. Cikin 'yan kwanakin da Sulaiman yayi a garin *Dabi* yayi sune cikin takurewar zuciya gami da tsananin damuwa mutukar zai bud'e ido ya dinga ganin Sayyada a matsayin matar d'an uwansa zai ji kamar zuciyarsa zatayi buga saboda takaici da 'bakin ciki a ganinsa sam! Sayyada bata dace da Sadam! ba dashi ta dace, sai kawai ma ya dinga jin tsanar d'an uwan nasa na d'arsuwa a cikin zuciyarsa a daddafe yayi kwana biyar ya had'a kayansa yayi musu sallama ya tafi......Wannan karon Sayyada bata damu da tafiyarsa ba kamar da inda duk sanda yazo garin to da kuka suke rabuwa da juna, al'amarin sai ya bashi mamaki! mutuka ya lura yarinyar na masifar son Sadam! ganin irin rawar jikin da takeyi kwata-kwata ma bata zama suyi hira kamar da zuciyarsa ta cika fal da takaici da bakin ciki had'e da masifaffan kishin 'Dan uwansa a duniya yana ganin bashi da babban ma'kiyi sama dashi. **** Sadam! kam tunda ya koma bakin aiki ya manta da wata Sayyada tinda dama can ba itace a gabansa da ita da babu duk d'aya suke a gurinsa babban abunda yafi damunsa shine yanda zai d'aukota ya ajeta cikin brecck d'insu wanda ya tara mutane mabambamta ra'ayi da addini kowa yana yin abinda ya ga dama duk kuwa da cewar wasu daga cikin su akwai iyalinsu a ciki hakan baya hanasu shaye-shayen su da neman mata idan ta kama suje club ranar da suke hutu haka kowanne zai fita cikin mota wasu su dawo wasu kuma su kwana can marasa kunyar cikinsu kuwa har mata suke kawowa al'amarin dai ya 'kazanta babban abinda yake tunani kenan zaman Sayyada a bracck din yasan halinta da shegen rawar kan tsiya kuma duk da ba wani sonta yake ba to dole ne yayi kishin auransa sam! baya so wani shege ya kalleta balle ya 'kyasa....! Sadam mutum ne mai kawaici da kau da kai ga abinda bai shafeshi ba shiyasa suke ganin mutuncinsa shaye-shaye da neman mata duk Allah ya tsare shi kawai ku barshi da busa haya'kin sigari yana shanta sosai mussaman idan yana cikin 'bacin rai! le'bansa ya d'an soma ba'ki kad'an amma sai wanda ya 'kura ido yake ganewa sam baya shan sigari a idon jama'a shiyasa iyayensa basu taba sanin yana sha ba kuma baya ta'ba yarda kaji warinta a jikinsa mutum ne mai tsaftar gaske kuma yana da ri'kon addini dai-dai gwargwado sai dai fa mugun muskili ne wanda baka ta'ba sanin abinda ke cikinsa saboda tsabar zurfin ciki ko yana son abu baya ta'ba nunawa komai yana bi a sannu baya rawar kai.....Ga yanayin 'kwayar idanunsa zaku gane cewar shi d'in mutun ne mabukaci ina nufin mutum ne mai yawan sha'awa shiyasa yake yawaita azimi saboda wannan matsalar amma saboda tsabar cutar kai ya'ki ya tsaya ya kalli mace ma ballanta yayi tunanin aure....Duk cikin family d'insu shi kad'ai ne ba'ki shima ya d'auko fatar mahaifiyarsa ne kasancewar ta 'yar asalin garin Maiduguri kasuwanci ya kawo mahaifinta Kaduna amma yawanci danginta na can barno da zama Hajiya Fatsima tana da kyau sosai sai dai 'bakace Sadam! sai ya dauko yanayin fatar ta amma kuma ya fita haske saboda shi tasa fatar sai ta kasance tamkar ta ba'ka'ken turawa black America yana da dogon hanci da manya idanu wanda kusan kullum suke a lumshe sai yana filin daga sannan za kaga ainihin hallitar idanunsa amma haka kawai gari banxa baka isa kaga ya ware maka dukanin idanunsa ba ko kallon mutum zaiyi ta 'kasan ido yake kallonka saboda tsabar munafurci haka duk yake 'karewa matan mutane kallo dake yana da yalwar gashin ido idan yana kallonka baza ka ta'ba ganewa ba.....Dogo ne shi amma ba sosai ba yana da fad'in kirji da murd'ad'an jiki wanda yasha training sannan jikinsa du gargasa ce mussaman kirjinsa da kafafunsa kusan kullum cikin gyaran fuska yake saboda yanayin hallitarsa domin ita kanta sumar kansa abin kallo ce yana bala'in ji da ita da kashe mata kudi wanda baza su ta'ba lisaafuwa ba. Sayyada Fara ce tas saboda tsabar haskenta har yalo takeyi mussaman idan taji rana to ita abun ne ya had'e mata biyu can bangaran mahaifinta fulani ne suma sannan bangaran babarta ma haka shiyasa abin yayi mata yawa tana da gashi sosai gashi ba'ki mai santsin tsiya wanda ko kitso ma ba ya zama a jikinda sai dai kawai ta gyara tayi gammo dashi......Siririya ce tamkar ka bushe ta ta fad'i amma kuma idan ka kalli yanayin jikinta mussaman tsintsiyar hannunta da zara zaran yatsunta zaka fahimci cewa gaba kad'an idan ta samu kulawa da abinda take so zata cika ta batse.....Tana da wani irin sharp mai fizgar hankali cikinta a shafe tamkar bata cin abinci sai dai kas! babu nonowan arziki a kirjinta kananu ne wanda itama duk kankantar hannunta baza su cika su ba, Ko da yake ai akwai sauran shekaru a gaba zasu fito sosai. Sayyada mai kyauce wanda kallo daya kayi mata zaka so ka sake kallonta tana da kyawu bayyanan ne kewayayyiar fuskarta na dauke da dogon hancinsa sa siraran le'bunanta masu d'an tudu kad'an bata da manya ido sosai sai da Allah ya wadata ta gashin gira dana ido gazar gazar dasu abin sha'awa idonta kamar tasa sanya kwalli shiyasa sam bata damun kanta da lallai in tayi wanka tasa kwalli ba saboda ita Allah ya zana mata a idonta. Sayyada nada rawar kai sosai bata cuta amma ba yarda a cuceta ba Allah ya sanya mata kauna da son Sadam! tun bata kai shekarun haka ba take sonsa idan yazo garin takan shiga cikin wani yanayi mai dadi haka kurrum yanayinsa da yanda yake tafiyar da rayuwarsa yake burgeta tsaftarsa da kamun kansa na burgeta da bata sha'awa tun lokacin data girma taji labarin auransu tayi ta murna da farin ciki tana fadin mutukar ta auri Sadam ta gama dace da mijin aure. **** Sulaiman fari ne tas dogo dan ya d'ara Sadam a tsayi sai dai Sadam din ya fishi cika ido Sulaiman kyakkyawa ne ajin farko kuma dan boko ne duk a 'kidunsa na nasara ne domin ma bai cika tu'ammali da manya kaya ba sai da kananu Yayi aure shekaru biyar da suka wuce matarsa ko 'batan wata bata ta'ba yi ba sai wannan karon ta samu ciki yanzu dai cikin nata nada watanni takwas. Amina tana da hankali da nutsuwa ta girmi Sayyada da shekeru uku shiyasa tafita hankali Amina gajera ce bata kai tsayin Sayyada ba amma tana da kirar jiki mai kyau fatarta luwai luwai sannan Allah ya wadata ta da nono masu daukar hankali tana da sauki hali mutuka don magana ma bata dame ta ba, ba kamar Sayyada ba da in tana guri sai ta gundiri jama'a. A tsakaninsu akwai sha'kuwa sosai da fahintar juna Amma tun sanda Sayyada ta lura da yanda Aminar ke shishshigewa Sadam yasa taji ta soma tsanarta Sai ta rage shiga kofarsu sai dai Aminar ta shigo to idan ma ta shigo kofar tasu Sayyada watarana basa wanyewa lafiya da fada suke rabuwa. Duk Wasu abubuwa na bukatar rayuwa Alhaji Auwal da 'yayansa na kokarin ganin sun kawo musu don haka basu da matsalar abinci da abun bukatar rayuwa Baba Ladidi ce kawai 'yar rigima ita lallai sai ta dorawa Sayyada tallah,ita kuwa Baba Marka tana kad'a lagwanin risho ne 'yan yaran matan dake unguwar wanda basa aiki da itace suke siya wannan shine sana'ar da takeyi daga zaune. itama Baba Ladidin ganin Sayyadar ne yasa take d'ora mata tallah amma da babu ita dole ne ta hakura tayi sana'a irinta Baba Ladidi. Wannan kenan. **** Yana zaune a ofis Captain Habu ya shigo hannu ya bashi suka gaisa kana ya zauna kujerar dake fuskantarshi hankici ya ciro daga aljihunsa ya goge gomin fuskarshi ya kai kallonsa kan Sadam! da yake faman duba wasu takardu yace."Wai ya zamuyi ne da tafiyar da take tun karo mu kasan Allah ni jin tsoron tunkarar wannan 'kauyen da babu wani dan adam din da yake rayuwa a cikinsa Ina jin tsoron mutanan sosai domin sharrinsu yafi na tsohowar mota." Ya d'ago kansa yana kallonsa fuskar nan a murtuke yace."Wai ke me yasa kake hakane? tamkar ba namiji ba kar fa ka manta da cewar wannan aikin da kakeyi ka dauke shi ne da al'kawari ko kashe ko a kashe ka gabakidaya rayuwarka kar ka sanyata a ranka komai zakayi to kayi da zuciya d'aya tare da taimakon neman taimakon Allah, ladanka yana gurin Ubangiji Sannan kuma ka daina jin tsoron wani hallita in ba Allah ba Allah da manzonsa su kadai ne suka cancanta da muji tsoro ba wata hallita ba, ni ka ganni ko Wallahi Wallahi! Wallahi! kaji nayi maka rantsuwa sau uku ko!? mutukar kaga ba'ayi wannan tafiya dani ba to bana nuffashi a doron duniya, a yanzu babu abinda yake gabana sai tunanin yaya za'ayi mu ci galaba kan wad'annan azzaliman mutanan." Captain Habu ya girgiza kai yana kallon Abokin nasa yace." A gaskiya ni ina jin in shigar da uzirina gurin Yalla'bai domin jikina na bani gagarimun al'amari zai faru kaga ni ina da iyali da yara gwara kai baka aje kowa ba kuma a zahirance kai ka fimu taurin zuciya da jajurcewa da hikimar ya'ki ina ganin zaka iya tseratar da ranka in wata matsala ta afku" Murmushin takaici yayi ya aje biron dake hannunsa yace."Wai Habu don Allah waye meyi ne."? Habu yace."Allah ne." Sadam! yace."To amma ka kasan da haka ka kasa yin tawakalli ka bar masa lamarinsa, idan fa mutuwa kake tsoro to ko kaje ya'ki ko ba kaje ya'ki ba idan lokacin ka yayi sai ka mutu gwara ma a kashe ka gurun ya'ki kasan kayi jihadi makomarka Aljanna kuma kana maganar Iyali ni waye ya fad'a maka bani da iyali ina mai tabbatar maka da cewar yau saura sati biyu kacal daurin aure na." Captain Habu yayi saurin d'ago kai yana kallonsa da mamaki a tare dashi....Sadam! ya d'aga masa kai yana so ya tabbatar masa da gaskiyar magana yace."Iyayana sun had'ani aure da 'kanwata dake can garinmu *Dabi* So kaga magana Iyali ba kai kad'ai zakayi ba har dani." Habu yace."Amma wannan magana ta bani mamaki wallahi wato kai da sai ranar daurin auran sannan ne zaka sanar damu."? Ta'be baki yayi yace."Auran ne bana so kawai shiyasa sam! bana d'okinsa har so nake lokacin tafiyar yazo in matsa in basu guri." Captain Habu yace."Amma ka bani mamaki wallahi!!! Sadam! murmishi kawai yayi baice komai ba, Habu yace."In tambaye ka mana." Yace."Ina sauraronka." Yace."Yanzu ya zakayi da Halima idan taji maganar auranka baka tunanin abinda zai faru da ita."? Sadam! ya 'bata fuskarsa yace."Wai shin Habu ni nake son Halima ko kuma ita ke sona."!? Captain Habu yace."Itace take sonka." Sai ya d'aga kafad'a yana ya mutsa fuska yace."To kagani ni banda matsala tunda dai ni da bakina ba'a ta'baji nace ina sonta ba ballanta kuce na yaudareta itake yaudarar kanta tunda tasan ni ba mahaukaci bane da zan aureta bayan kowa ya mayar da ita rigar sanyawarsa Kawai ina biye mata ne saboda darajar son da take min wannan shine dalili." Captain Habu ya girgiza kai yace."Tabbas to amma ni ina tunanin al'amarin da zai faru taji labarin auranka wallahi zata iya kashe kanta saboda bakin ciki." Sadam! yasa dariya yana kallon abokin nasa yace."Na lura kana tausayawa Halima da yawa kaje kawai ka aureta na bar maka kai nifa har yanzu banga wata 'ya macen da zata ya mutsa min tunani ba wallahi idan ba Uwata ba bana daukar wata mace wani abu saboda dukaninsu basu da kirki.'' Sulaiman yace."Me yayi zafi kake wannan maganar mace ni'ima ce ga d'a namiji sa'ida ce kuma salama ce ba zaka san da haka ba sai ranar da kayi aure sannan zaka gane abinda nake so ka gane." Murmushi kawai yayi Habu yace."Don Allah abokina ka dinga 'kimanta mata kuma idan na baka shawara ka dinga dauka kamar yanda idan ka bani shawara nake dauka." Yace."To na dauka." Habu yace."To yanzu yaushe zaka kaini inga amaryar tamu."? 'Bata fuska yayi yace."Kaji ka da wani zance kuma ka bari kawai ai in an daura auran nan zan kawo ta kaduna." Yace."A'a dole fa kafin daurin aure muje in ganta gaskiyar magana kenan.'' Okey Zamu je insha Allah sati me zuwa."! Habu yace."Allah ya kaimu lafiya." To da wannan magana sukayi sallama Captain Habu yayi masa sallama ya koma ofis din sa. ***** Sulaiman kuwa bayan komawarsa Kaduna sai da yayi jinyar zuciyarsa na sati guda sannan ya shirya tsaf ya nufi kasar india domin cigaba da gudanar da harkokinsa na kasuwanci Sulaiman komai da ruwanka ne shi ko wace sana'a tashi ce ya fita 'kasashen waje da dama domin gudanar da harkokinsa shiyasa kullum Allah yake kara yalwata masa arzkinsa gashi yana d'an ta'ba siyasa in lokacinta yazo. Da tunanin Sayyada ya nufi 'kasar hindu. **** Sayyada fa ananan ana rawar kai da giringid'ishi kullum ana gidan Mariya ana maganar aure ita kuma mariyar in ta kad'a magani da madara na 'karin ni'ima sai ta tsiyayawa Sayyadar tace ta shanye duk sanda mijinta ya soma kwanciyar aure da ita zaji dad'inta aikuwa Sayyada ta bada himma har ta zo gida tana fad'awa Baba Ladi tace"Ta had'a mata maganin Ni'ima wanda Sadam! zai dinga gamsuwa da ita yayin kwanciyar aure. Baba Ladi da Baba Marka suka dinga salati da sallalami! Baba Ladi tace"Don Ubanki a ina kikaji waannan maganar." ? babu kunya tace"Mariya ce ta fad'a mata. Tundaga ranar Baba Ladi ta hanata fita tace tana zuwa gidan Mariya tana koya mata rashin kunya.....Sayyada kam! tace"Lallai Baba kar! kar! nake kallon kowa idan Baba Ladi ta idar da sallahar walha bacci ya kwashe ta sai ta lalla'ba ta fice daga gidan bata dawowa sai yamma Baba Ladidi ta dinga fad'a kamar ta ari baki. Suna zaune a tsakiyar dakin Mariya Ummi ta shigo sai suka hau shewa harda tafawa Ummi tace"Wace wainar kuke toyawa ne? Sayyada akayi wani fari da ido akace "Ke ma kin san wainar."! Ummi ta bata hannu suka tafa suna dariya. Mariya tace" Wai Ummi kinji so ta take ta samu maganin da zai 'kara mata girman nono saboda tana so ya dinga cikawa angon nata hannu." Sai suka kwashe da dariya Sayyada tace"Wallahi da gaske nakeyi ni kunya nakeji duba fa ki gani nono kananu ne ko rigar nono bana sawa fa." Ummi tace"Ke Dallah! banza kawai Wallahi ki kwantar da hankalinki nononki zai fito yayinda aka kai ki gidan miji shikkenan kullum idan yana ta'bawa shikkenan sai dai kiga suna girma sun cika riga." Sayyada ta bata hannu suka tafa tace"Da gaske kike don Allah."? Ummi tace"Wallahi da gaske nake." Mariya tace"Hakane nima fa lokacin da aka kawo ni gidanan ba nonon arziki gareni ba amma ko wata uku banyi ba naga nonowana sunyi manya manya." Dariya sukayi suka tafa Sayyada tace"Wayyo Allah na ni wallahi har na 'kagara lokacin nan yazo wai don Allah Mariya yaya mutum yake ji idan yana sha'awar d'a namiji wayyo."!!!!!!! Ta kare maganar tana kwanciya tare da lumshe ido. Ummi tace"Kai! Sayyada gaskiya ke fitananniya ce anya kuwa."!?? Sayyada ta kai mata duka tana dariya tace"Ke sonsa ne kawai yayi min yawa shiyasa sai kunyi min uziri." Mariya tace"Wai yaushe zamu ganshi ne nifa ban san shi ba nafi sanin Yaya Sulaiman."! Ummi tace"Wallahi nima ban sanshi ba jikina na bani kyakkyawa ne dan gayu." Sayyada aka lumshe ido ana murmushi mi'kewa tayi zaune tace"Sojana kenan." Suka kalleta gabadaya sukace "Au! Soja ne dama."!? Daga kai tayi tace " Eh mana ai ba zaku gane shi ba tunda ba sosai yake zuwa ba sannan kuma idan yazo baya dad'ewa yake tafiya watarana ma yini guda yake ya tafi sannan shi bashi da fara'a kamar Yaya Sulaiman kullum fuskarsa a murtuke take nima fa baya wani sakar min fuska." Mariya tace"Ai dole mana Amina tace shi take so shegiya ni wallahi haushinta ma nakeji." Sayyada taja tsaki tare da fad'in"Rabu da tsinanniya kawai ai tuntuni na daina kulata." Mariya tace"Kinyi min dai-dai 'kawata." Tafawa sukayi suna dariya *To ni dai fitowa nayi na barsu na lura hirar tasu ba zata 'kare ba* ***** Sayyada sam! bata sanya Amina cikin sabgarta da kawayenta kawai take harka ko Aminar ce ta shigo kofar su Sayyada ba tayi mata kallon arziki Ballanta ta kulata Baba Ladi tayi mata fad'a har ta gaji......Wannan lamari na masifar 'batawa Amina rai! shin wai meye duniyar ne akan Namiji Sayyada duk ta tayar da hankalinta tana gaba da ita itafa bata zafafa ba duk da tana son Sadam! to idan shi baya sonta ya zatayi dole ta hakura kuma idan yace ba zai aureta ba nan ma dole ta hakura ta fito da mijin aure ita a ganinta wannan ba abun tayar da hankali bane. To ammafa a cikin ranta tanan da wannan kudiri na duk sanda Sadam! d'in ya shigo garin zata sanar masa halin da take ciki a kansa tasan idan ya hadasu duka ya aura ai ba haramun ya aikata ba. **** Saura Sati guda daurin aure Baba Ladi da baba Marka tsaye gaban wani katon turmi me zurfi ko wanne da ta'barya mai tsayi a hannunsa dagab tukud'i suke da gumbar mata. Tsaf! suka daka suka kwashe sannan suka zauna zaman had'awa! lokacin Sayyada nacan gidan Mariya wai nan dilka ake da kurkur Mariya ta dage! tana wa Sayyada dilka wai lallai sai tayi kyau kafin Ranar daurin aure. Amina ce ta shiga kofar taga abinda sukeyi tace"Baba Wannan meye?"? Baba Marka tace"Zaki san ko meye idan lokacinki yazo maza kije gidan Mariya ki kirawo Sayyada." Amina tace"To." Ta nufi gidan Mariya dake bayan layi. Tsakar gida ta tarar dasu sunyi d'an malele da yaji da manja harda tumatiri da albasa suna sha suna dariya da hirar aure kamar yanda suka saba. Babu wacce ta amsa gaisuwarta sai kallon banza da suka watsa mata Amina tace"Sayyada kije Baba Ladidi na kiranki." Ta juya zata fita Sai taji Sayyada na kwaikwaiyar maganar ta da hanci "Wai Sayyada kije Baba Ladidi na kiranki yan! yan! yan!!!!! Ta juyo tana kallonsu sai suka kwashe da dariya Amina ta bar gidan da sauri takaici kamar ya kasheta wai Sayyada ce take biyewa wasu bare suna wulakantata......Sayyada ta wanke hannunta tare da zura hijab dinta tace" Bari naje na dawo yanzu." takalmanta tasa ta fice daga gidan. Amina ta hango tana tafiya so take ta isketa har inda take ta ci mata Uwa! tana karya kwana taga motar da ya saba zuwa da ita garin tayi parking irin motocin nan ne na gurin aiki.Kafin ta an kara Taga ya fito daga motar tare da Abokinsa sai gabanta ya hau dukan uku uku! ta hau kallon jikinta wani ko d'ad'd'an zanin atamfa ne a jikinta da wata t_shirt mai karamin hannu kanta ko d'ankwali babu sai hijab data zurma "Wallahi ba zai ganni a haka ba." a fili tayi wannan maganar la'bewa tayi tana le'kensu inda taga Amina ta iskesu ta tsuguna har 'kasa ta gaishesu, girgiza kai tayi haushi ya turnuketa tana kallon sanda Yake amsawa yana mata dariyarsa mai tsada Sayyada kamar ta kurma ihu! sai cije baki take tana gyada kai tana kallonsu suka nufi cikin gidan tare........Sai bayan taga shigewarsu ne sannan ta fito daga inda ta 'buya. Gidan ta nufa duk ranta babu dadi. 6/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ *Free Pege 13* Cike da farin ciki Baba Marka take fad'in"Sannuku da zuwa sannu kunsha hanya ashe dai angon nawa yana tafe da har ina cewa zanzo biko ashe dai ana sane dani." Tabarma ta shimfida musu suka zauna Captain Habu sai murmushi yakeyi karamcin matar ke bashi sha'awa gaisawa sukayi a mutunce tana tambayar mutanan gida Sadam! ya kalli 'kofar dakin Baba Ladidi yace."Ina sauran mutanan gidan suke."!? Baba Marka tace"Baba Ladidi dai bata dad'e da fita kasuwa ba ita kuma Sayyada yanzu yanzu na aika kiranta tana gidan Kawarta Mariya." Ta kalli Amina dake tsaye tace"Ina Sayyadar."? Amina tace"Tana kan hanya." Kafin Baba Marka tace wani abu Sayyada ta shigo bakinta dauke da sallama. Baba Marka tace"Yawwa gatanan ma." Sayyada ta karaso inda suke fuska babu yabo babu fallasa take gaishe su, Sadam! ya kalleta yana wani ya mutsa fuska sam! bai amsa gaisuwar ta ba Captain Habu ne ya amsa da fara'a a fuskarsa Sadam yaji takaicin yanda Habu yaga sayyada kaca-kaca duk da cewar bai tabbatar da cewar itace ba. Dakin Baba Ladidi ta shiga ta cire kayan jikinta dogon hijab ta sanya har kasa ta fito kai tsaye bakin rijiya ta nufa ta jawo ruwa cikin rijiya bandaki ta nufa tayi wanka tana fitowa idanunsu suka game da juna yayi saurin kauda kansa yana kur'bar damammiyar furar da Baba Marka ta damo musu Baba Ladidi ce tayi sallama ta shigo hannunta rike da wani buhu mayafi a saman ka tace"Ai tunda na doso bakin layi na hango motar sojoji a kafe nace to Soja yazo ganin amaryar tasa." Ta karashe maganar tana dariya hade da kokarin aje buhun a gefe ta cire mayafin dake saman kanta tana fad'in"Ai fa wannan ranar dama nasan dole ne ta tambaye ni." Baba Marka tace"Ai sai da na fad'a miki cewar ki bari ranar tayi sanyi in yaso sai ki tafi." Ya d'ago kansa a nutse yana kallonta yace."Wai shin ma ina taje da wannan ranar."!? Baba Marka tace"Haba kaiko sai kace wani kurma kana ji fa nace kasuwa ta tafi." Ya kalli Baba Ladidi dake firfita da mafici yace."Baba ashe dai baki fasa yawon kasuwar nan ba ko."!? "Oo! ni ba abinda kake tunani ne ya kaini kasuwa ba ato tawa ce ta kaini ta wani gefan kuma sai in ce ta dalilin ka na shiga kasuwar." Ta'be bakinsa yayi ya mayar da kansa 'kasa Baba Ladidi ta washe baki tana kallon captain Habu tace"Ashe tare kake da ba'ko sannu da zuwa samari ya mutan gida da fatan duk sunannan lafiya ko."? Captain Habu yace."Kowa lafiya lau ai sunce ma a gaisheku da kyau."! Baba Ladidi tace" Alhamdullhi ." Sai ta fara zazzage abinda ke cikin buhun tana dubawa tace"Kinga na samo saiwowin maganin nan da duk abinda ake bukata saboda haka yanzu yanzu zan sanya 'Dantani ya yanka min kazar." Baba Marka tace"Hakan yayi sai ya had'a da Zabi gudu uku ya yankawa ba'ki ayi musu miya ko."!? Tace"Kwarai kuwa kinga kuwa naga kayan miya masu kyau a kasuwa wallahi wannan ranar da ake kwalawa itace ta hanani na tsaya na siyo." "Aifa! gwara da kika nufo gida a aika Dantani ya siyo yanzu." Baba Marka tafada tana kokarin mikewa mayafi ta dauko jikin kyauran dakinta ta yafa ta fito tana fad'in"Bari in kira Dantani d'in nasan dai yanzu ya dawo cin abinci daga gurin sana'arshi." Har ta kai kofar fita Baba Ladidi tace"Wai Ina Sayyada ne? ko bata dawo daga gidan kawar tata ba." Marka tace"Shigowarki ta shiga daki tana ciki tana jinki." Labule ta d'aga ta fito Tana sanye da riga da siket na atamfa soso tayi wata irin kwalliya ta d'ige-d'ige a da kwalli kumatunta da saman goshinta sai le'banta data mulke shi da jan janbaki fuskar nan jazur da jar hoda abinka da farar fata. kanta babu dankwali sai ubangashi data daure shi a tsakiyar kai yana reto ga wani uban kyalli da yake saboda man data lafta masa Sadam! na ganinta ta fito a haka ransa ya 'baci indai ba idonsa ne ke masa gizo ba har cibiyar ta sai da ya hango lokacin da take kokarin zama kusa da Baba dake rigar karama ce sannan hannunta me fad'i ne wanda tana d'agawa za'a iya ganin hamtarta Gashi kanta babu dankwali duk ta fito da surar jikinta, Rai a 'bace ya daka tsawa tare da fad'in"Maza ki tashi ki sanjo kaya wannan ai sun matse ki sannan dake ke mara hankali ce kin fito babu dankwali wai ke kinyi ado." Cikin jin haushi ta watsa masa harara! ta dauke kanta tana zumbura baki. Baba Ladidi tace"Dad'ina da kai kenan kai ba'ayi maka gwaninta a maimakon ka yaba da kwalliyar da tayi maka sai ka kushe hakan bai dace ba." Ta kalli Captain Habu tace"Don Allah ka dinga bawa abokinka shawara ya rage fad'a! da jarabar masifa yarinyar nan dai marainiya ce." Captain Habu yayi dariya yana d'an kallon Sayyada ta 'kasan Ido gaskiya abokinsa yayi dace da mace nan gaba kad'an yasan yarinyar zata zama cikakkiyar mace. Yace."Muma can gurin aikin haka muke fama dashi Baba Sadam! din ne ai ya cika zafi shiyasa ko a filin daga! ba'a cin galaba a kanmu."! Baba Ladidi tayi dariya tana fad'in"Ai filin ya'ki daban damu da iyalinsa bana so a daura aure yazo ya tsawalawa yarinyar mutane." Captain Habu yace."Karkiji komai Baba insha Allahu zamu rike Sayyada da kyau da kulawa." Baba tace"To nagode Mai gidana na kaina."! Mikewa tayi ta shige d'aki Sayyada ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da 'yan ya tsunta na hannu Sadam! sai dalla! mata harara yake yana ya mutsa fuska. Shi ko Captain Habu sai janta yake da wasa tana murmushi. Tsaki yayi yace"Wai don Allah Captain me ka hango naso a jikin wannan yarinyar ne? dube ta da kyau ka gani in banda iyaye iyayene Allah da ba zan takurawa kaina ba Duk tsiya nasan Halima ta fita komai da komai."!!! Sayyada ta d'ago kai ta kalleshi ranta ya 'baci idanunta suka kawo ruwa wacece kuma Halima? Captain Habu ya 'bata fuska yana fad'in"Aboki meye haka wannan ai cin fuska ne." Sadam! ya kauda kansa gefe waya ya ciro yana dubawa "Kiyi hakuri kinji amarya." Captain Habu ya fada da kokarin ganin ta saki fuskarta, Kallonsa tayi tace"Abokinka yace bai ga abinso a tare dani ba Allah yasa bashi kad'ai gareni ba ko yanzu yace baya so akwai dubanninsa masu so saboda haka nima ba wai sonsa nake ba Umarnin magabatana kawai nake bi." Tana gama maganarta ta mike ta shige daki hijab ta zura ta fito Baba Na daki tana fad'in"Sayyada kar ki fita ina zakije dawo ki shanye maganin nan na dama miki kar ki fita fa." "Baba nifa na tafi gidan su Ummi domin ba zan zauna a cikin gidan nan ba mutukar yana cikinsa sai ya tafi na dawo." Tana gama maganarta ta fuce daga gidan cikin bakin ciki da takaici, tana daf da fita babban soro suka ci karo da Amina hannunta rike da wata leda da alama daga shagon Magaji take lemon kwalba ne fenta da mirinda ta siyi da sanyi 'kara-'kara!! Sayyada ta tare mata hanya rai a 'bace tace"Dama neman ki nake. Amina tace"Menene kuma."!? Sayyada ta rike 'kugu tana fad'in"Tambaya ta ma kike menene lallai ma Amina! dan kutumar ubanki wannan lemon ubanwa kika siyowa? Amina tace"Kar dai ki sake ki zageni Sayyada lemo kuma babu ruwanki da wanda na siyowa! Wallahi sai naji Uban da kika siyowa lemo sannan me zakiyi idan na zage ki." ? Amina tayi murmushi tana kokarin ratse ta ta wuce tace"Ni dai ba karya bace da zan zauna ina haus........Ai kafin ta 'karisa Sayyada ta buga tsalle ta kaud'a mata mari! "Nice karya dan babanki." Sai ta wafce ledar hannunta a take kwalbar lemukan suka fashe lemon ya zube a kasan gurin......Kwalbar lemon da ta fashe ta d'auka tayi kan Amina tana huci! wallahi sai nayi miki zane a fuskarki ni zaki kira karya ki shiga gonata ki kirani karya lallai Amina kin ta'bowa kanki bala'i! Amina da taga Sayyada na nema ta lahanta ta sai ta fara neman hanyar tserewa Sayyada ta jawo hijab dinta wanda gari jawo hijab din ta taka karamar kwalba a take ta huda mata kafa amma ko a jikinta kokari kawai take tayiwa Amina zane a fuska.....Ihu! Amina take tana fad'in "Wai Sayyada ke mahaukaciyar ina ce ne? me nayi miki.? A fusace tace" Mahaukaciyar gidaj Ubank....Kafin ta karasa taji saukar mari a fuskarta Yana tsaye ransa a 'bace yace"Sakar mata hijab." Sai ta rushe da kuka tana fad'in"Ai kamata yayi kafin ka yanke hukunci ka tambayi ba'asi kawai sai ka mareni alhalin itace da rashin gaskiya." Hararta yayi yace"Ban tambaye ki komai ba saketa ki wuce cikin gida." Sayyada ta sakar mata hijab Ya kalli Amina dake motsa baki yace."Ke Amina meye ya had'aku."? "Wallahi Yaya Sadam! ban san abinda nayi mata ba kawai karo mukaci tazo fita ni kuma zan shigo naje shagon Magaji na siyo muku lemo shine fa ta tareni da kokawa tana zagina." Ya kalli Sayyada rai a bace! zai hau surfa bala'i Captain Habu yace."A'a ba haka ake ba ai kaji magana daga bakin Amina itama sai ka fara jin ta bakinta haka ake hukunci." Hararasa yayi yace."Baka san halin wannan yarinyar bane Habu Sayyada batajin magana wallahi nasan itace da tsokana." Captain habu yace."Eh duk da haka dai kaji ta bakinta." Ya jiyo da hankalinsa kanta ganin jinin dake fita daga hannunta yasa jikinsa yin sanyi ya kura mata ido a hankali yace."Meye ya had'aku?" "Itace take cewa dani Karya shine nace sai ta fad'a min inda nayi karuwanci tunda dai ni nasan karuwa kawai ake kira da wannan kalmar." Sadam! yaji takaicin wannan kalmar ta Karya ya kalli Amina da jan ido yace."Amina da hankalinki kike kiran 'yar uwarki da wannan kalmar."!? Amina tayi rau!rau! da ido tace"Wallahi zuciya ce ta ciyo ni kuma Sayyada ta dad'e tana min abubuwa shiyasa ban san sanda na kirata da wannan suna ba." Yace."To daga yau sai yau kar ki sake kiranta da wannan kalmar kinji ko." Tace."To insha Allahu." "Ko wacce ta shige 'kofae su." Sayyada ta kalli Amina tana mata gwalo Amina tayi rau! rau! da ido tana kallon Sadam din da ya juya baya da niyar barin gurin tace"Yaya Sadam! idan anjima akwai wata magana da zamuyi da kai." Sayyada tayi saurin juyowa tana kallonta Amina ta dauke kanta Sadam din yace."To babu laifi Allah ya kaimu lafiya." Fita sukayi shida Captain Habu, Ita kuma Amina ta juya zata shiga kofar su Sayyada tace"Banza jaka mayya kawai Wallahi duk nacin ki sai dai ki hakura banza kawai."!!! Amina ko waigowa ba tayi ba ta shige kofarsu tana addua Allah yasa hakanta ya cimma ruwa.....Sayyada ta jima a tsaye a gurin tana sake sake daga bisani ta nufi babbar kofa aifa ba zata basa zuwa gidansu Ummi ba sai dai kome zaiyi sai dai yayi. 7/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ *Free Pege14* Koda Sayyada ta fita can ta hangosu tsallake kan wata katuwar tabarma tare da matasan samarin garin irin su malam Bashir, dauke kanta tayi tazo ta wuce ta gabansu Sadam! ya bita da kallo yana girgiza kansa kafin ya ankara ya hango Talle ya tare mata hanya harda dogare hannunsa a jikin bango magana yake mata kasa-kasa ita kuma sai waiwayen bayanta take tsoro take ji kar yayiwa Talle ilah! dan ga dukanin alamu Talle ya mance karonsu dashi......"Haba baby yawa kikeyi karfa ki manta da cewar ni masoyinki ne me kaunarki a cikin ko wane hali.' Sayyada ta juya tana kallon bayanta aikuwa sai ta hangoshi yana tafiya tamkar wani zaki har ya kusa riskarsu....."Wai baby kallon me kikeyi ni nefa Talle masoyin......Yana ganin Sadam! sai ya sunkuyar da kansa kasa hanyar fecewa yake nema Sadam ya 'karasa gurin tare da tare masa hanya fuskarsa babu annuri yace."Kai tsami guy ya kake? wato ka manta gargadin da nayi maka kwanakin baya da suka wuce ko."? Talle yayi kasa da kansa tsoro duk ya dabaibaye shi mussaman da ya lura da wandon sojojin dake jikin Sadam! Baki na rawa yace."Ayi hakuri yallabai soyayya ce ta jawo." Sadam! yayi murmushin takaici yace."To kaje ka nemi dai-dai da kai domin wannan dake tsaye a gabanka ba sa'ar auranka bace." Baki na rawa Talle yace."Insha Allahu na daina kulata daga yau na fahimci komai." Sadam! yace."Kai dai ka sani na fad'a maka duk ranar da na sake ganin ka nuna ka santa ranar zaka 'bakunci lahira." Talle ya dinga bashi hakuri kokari kawai yake ya bashi hanya ya wuce. Talle na barin gurin ya mai da hankalinsa kanta. Kasa tayi da kanta gabanta na fad'uwa yace."Ina zakiji ba cewa nayi ki koma gida ba."? Baki na rawa tace" Gidan su Ummi zani." Ya watsa mata kallon banza "Wuce cikin gida ko ranki ya 'baci! Kafin ya ankara tayi gaba ta barshi a tsaye a gurin.....Baki a sake yake binta da kallo waigowa tayi tana kallonsa sai ta gumtse baki tana dariya ta juya ta cigaba da tafiyarta. Ya jima a tsaye yana mamaki! Wato yarinyar nan ta raina shi da yawa amma yasan maganinta zai daina shiga sabgarta tunda bata jin maganarsa. Majalisarsu ya koma cike da takaicin abinda Sayyada tayi masa. *** Can cikin gida kuwa Amina na shiga kofar su ta rushe da kuka Baba Iya na tatar gasara ta dakata tana kallon 'yar tata tace"Ke kuma lafiya? kin shigo kina kuka menene ya faru naga hannunki da hijab dinki da jini. Amina na share hawaye ta sanar da mahaifiyarta abunda ya faru tsakaninta da Sayyada Baba iya ranta ya 'baci ko wane lokaci Sayyada itace take cin galaba akan Amina amma ba'a ta'ba d'aukar mataki ba ana kallo Sayyada nayin abinda ta gadama a cikin gidan ba'a yi mata fada ita da take ma 'yar mace ba 'yar namiji ba gaskiya wannan karon ba zata yarda ba. Tana gama tatar gasarar ta dauki mayafi ta yafa ta nufi kofar su Sayyada.....Baba Ladidi na gaban murhu tana dahuwar kazar amare ita kuma Baba Marka na gyara kayan miyan da za'ayiwa su Sadam! farfesu Baba Iyatu ta shiga suka amsa sallamar ta Baba Iya taja ta tsaya tana fad'in"Baba Ladidi a gaskiya na gaji da irin wannsn abun da yake faruwa a gidan nan, Kullum Sayyada ke cin galaba akan Amina ba'a ta'ba daukar mataki ba haba abun yayi yawa gaskiyar magana ya kamata a gyara al'amarin yanzu gashi Sayyada ta farfasa mata hannu da kwalbar lemo jini sai zuba yake." Baba Ladidi tace"Subahanallahi! abinda ya faru kenan? Baba Iya tace"Kwarai kuwa baba gaskiya a jawa Sayyada kunne abinda takeyi yayi yawa." Baba Marka tace"To in banda abunki ma ai Sayyada ba maxauniya bace nan da 'yan kwanaki ta bar gidanan kuyi hakuri kan abinda tayi kuma za'a ja mata kunne." Baba Iya ta kama hanya ta fita tana bala'in jin takaici Sayyada zata riga 'yarta aure don dai babu yanda zatayi ne ta hakura shiyasa take so ta tayar da hankalin kowa a gidan kafin lokacin bikin. Ummi tace"Wai don Allah da gaske kikeyi Yaya Sadam! yazo." Sayyada tace"Lallai Ummi dama ina yi miki karya ne."? Ummi ta mike da sauri tana jan hannunta tace"Tashi muje na ganshi don Allah." Sayyada ta kalleta tace"Wai don Allah wannan rawar jikin da kikeyi na menene? ni bana son rashin kamun kai fa." Ummi tace"Wane irin rashin kamun kai mtwsss! dan ma kin samu zanje na ganshi na fasa zuwa." Sayyada tace"Yi hakuri tashi muje amma don Allah kiyi komai a nutse karki ta washe masa baki." Ummi tace"Wallahi Sayyada baki da mutunci." Dariya sukayi sannan suka fito tare Sayyada tayi wa babarsu Ummi sallama suka fita. Tun daga nesa Sayyada ke nuna mata shi Ummi sai kallon majalisar take tana so ta tantance waye Sadam! din Sayyada tace"gashi can me koriyat riga a jiki da wando irin na sojoji." Ummi tace"Na gane shi wai! gaskiya Sayyada kin dace da miji dan gayu dan birni gashi kuma soja." Sayyada akayi dariya, Sadam! takaici kamar ya kashe shi yana daga inda yake yana hango sayyada na nuno shi da hannu sai kace wata 'yar kauye dauke kansa yayi saboda tsabar bakin ciki Shi kuwa Captain Habu dariya kawai yake musu.........Garin kallon sa kafarta guda ta subce ta fad'a ramin kwata ihu!! ta kurma ta riko hannun Ummi! Yana kallon abinda ke faruwa yace"Allah shi 'kara dauke kansa yayi kuma baiyi niyyar mikewa ba....Habu ne ya mike da sauri ya isa gurin.....Yayi yayi ya jawo 'kafar Sayyada ya kasa sai kuka takeyi Ummi duk tayi kalar tausayi. Captain Habu ya isa inda yake zaune yace."Haba aboki ka tashi mana kaje ka ciro mata kafar Yarinyar nan fa garin son da take maka ne yasa ta fada cikin ramin haba mana." "Rabu da ita Habu idan ta gaji zata fito da kanta naji dadi data fad'a cikin ramin." Habu yace."baka da imani wallahi." komawa yayi gurin yana janyo hannunta ta ma'ke hannun kuka takeyi harda majina Captain habu ya koma gurinsa sai da ya nuna masa 'bacin ransa sannan ya mike ya iski gurin.....Tana ganinsa ta sake lanjarewa tana kuka kafar wandonsa ya tattare ya afka ramin Ba tare da wani bata lokaci ba ya sa'bata a kafad'arsa ya kama ya fito Sayyada rike shi tayi gam! tana sauke ajiyar zuciya....Ko da yayi nufin sauke ta sai ta'ki ta cikwikwiye masa riga hade da rike masa wuya dole haka ya hakura ya nufi cikin gidan da ita a kafadarsa. Baba Ladidi ta saka salati tana fad'in me zan gani Sayyada kwata kika fad'a."? Ya dure ta kasa ya kama hanyar bakin rijiya. Ruwa yaja ya wanke jikinsa ya nufi masaukinsa ya sanjo kaya, ya fito hannunsa rike da kayan da suka 'baci gabanta ya zubesu fuskar nan a murtuke yace."Gashi nan ki wanke min su tas! maganin mara jin magana kenan ni naji dad'i ma da kika fad'a rami da karyewa ma kikayi da kowa ya huta." Baba Ladi da baba marka suka sanya salati jin abinda ya fad'a! da sauri ya fice daga gidan yana dariya yasan idan ya zauna to zasu caccake shi Baba Ladi tace"Haba jama'a wannan 'kiyayya tayi yawa yarinya tsautsayi ya sameta amma kace dama karyewa tayi aikuwa ba fata akeyi ba ko karyewar tayi sai an daura auran nan in yaso sai ka ajiye aikinka kayi jinyar ta wannan ai mugun nufi ne kuma ka jibgo mata wanki kaya masu nauyi irin wannan kace ta wanke saboda rashin son gaskiya ni kam jikina ya soma sanyi da al'amarin nan." Baba Marka tace"Ai kin gani da yake ya san bashi da gaskiya ai ya gudu hummm! Allah dai ya kyauta shine abunda zamu ce." Ummi ta dinga matsawa Sayyada kafafunta har ta dan ji dadi kana ta zuba mata ruwa ta wanke jikinta ta sanjo wasu kayan ta fito tana fad'in"Baba banu Klein din da zanyi masa wankin." Baba Ladidi ta bude baki tana kallonta cike da mamaki tace"Ashe da gaske wankin zakiyi masa."!? Sayyada ta zumbura baki.Baba tace" Oo! ai ba hanaki nayi ba duba kan tagar can zakiga sabon omo ki dauko kiyi masa wankin dashi. Sayyada ta dauko Omo ta zuba ruwa tas! ta wanke masa t_shart dinsa da wandonta ta shanya su sannan ta wanke nata kayan da suka 'baci.....Ko da Baba ta gama dahuwar kazar amare Sayyada bata sha wahala gurin sayyada ba a take ta cinye rabin kazar baba ladidi taji dadi sauran da ta rage tace"Zata d'umama mata da safe. To kamar yanda yayiwa Amina alkawarin cewar bayan sallahar isha'i zai saurari maganarta hakane ta kasance Yanzu suna tare da ita a babbar kofar gidan a tsaye yace."Amina gani ina sauraran muhimiyar maganar da zamuyi dake." Kanta a kasa tace"Yaya Sadam! ba zan cuci kaina ba dalili kenan da yasa na yanke sha'awar fad'a maka abinda ke damuna shekara da shekaru." Shiru tayi tana me sunkuyar da kanta kasa yace."Ke nake sauraro Amina." Ya dan soma fahintar wani tace"Sonka nake da zuciya daya ina fatan zaka had'ani dani da 'yar uwata ka aura." A take yanayin fuskarsa ya sauya ya sha kunu sosai a fusace! yace."Ashe ni sa'an wasan ku ne ko Amina."!? girgixa kai tayi idanunta na kawo ruwa....Yace."To daga yau sai yau kar na kara jin wannan kalmar ta fito daga bakinki idan ba haka ba itama Sayyadar wallahi zan fasa auranta ko an fad'a muku ni sa'an auranku ne? Amina ta girgiza kai yace."Don kuna ganina ko da yaushe shiyasa kuka raina ni."!? girgiza kai tayi ya cigaba da cewa."Itama Sayyadar da ita da babu a gurina duk d'aya ne domin ni babu wata mace a gabana ta nace sai ta aureni sun nace! sai na aureta to babu abunda zasu tarar sai 'bacin rai da damuwa domin ni a yanzu ba wai auran ne a gabana ba dole suyi hakuri saboda haka ina me baki shawara da wuri kije ki sami miji dai-dai dake ki aura kar in kara jin wannan magana ta fito daga bakin ki." Kuka take tana bashi hakuri ko kallonta baiyi ba ya kad'a kai ya shige cikin gidan ransa a 'bace! Yana isa ya iske wani 'bacin ran Sayyada ya gani zaune gaban Captain Habu suna hira daga ira sai shimi mai siririn hannu kanta babu dankwali wani sashe na jikinta ma ana gani.....Idonsa ya kada yayi jawur...."Ke!! mara hankali."! maganarsa tasa suka juyo a razane!" "Tashi da Ubanki ko nazo nan na 'ballaki."!!! yana fad'a yana nuna yanda zai 'ballata da hannunsa. Da saurin ta mike yayi saurin rintse idonsa ganin gwiwowinta duk a waje....Ido jawur yake kallon Captain Habu da yasha jinin jikinsa!!! Jikinsa na kyarma! ya isa gurin 'kafa yasa ya harbe ta dashi ta 'kwala ihu!!! Baba Ladidi ta mike zaune da sauri tana mutsika ido tace"Wai hayaniyar me nake ji ne bacci ya soma daukana." Sayyada na kuka tace"Baba kinga abinda zai saka min dashi ko bayan na gama wanke masa kaya yazo yana dukana da kafarsa." Baba Ladidi ta kalleshi jikinsa sai kyarma yake tace"Wai meye ne? Sadam! don Allah ka dinga sanyaya zuciyarka me tayi maka."? ba tare da yace mata komai ba ya nuna mata hanyar d'aki cikin azababbiyar tsawar data tayar da Baba marka yace."Zaki wuce ko sai nayi filla!_filla! dake a nan gurin.'' Da gudu ta shige dakin Baba Ladidu ta afka kan gadon karfe tana kuka.......Masaukinsa ya shige yana wani irin huci!!! Baba Marka da Baba Ladidi suka dinga mayar da magana suna mamakin abinda ya jawo wannan hargagin! Shi kuwa Captain Habu tuntuni ya riga ya harbo jirgin.....Ya san mutuminsa yana da kishi sosai mussaman akan kansa da abinda yake so wannan ya nuna masa cewar yarinyar ba karamin matsayi take dashi ba a zuciyarsa........Baba Ladidi tace"Gaskiya Maigidana ka dinga tausar zuciyar abokinka bakin hali ne dashi." Habu ya dinga dariya yana basu hakuri sai da yaga ko wacce ta koma ta kwanta sannan yayi musu sallama yabi bayan Sadam! din masaukinsu. Yana shiga ya tarar dashi da karan sigari a hannu yana kokarin kunnawa fizgewa yayi yace"Zaka sha sigari a gidan tsofaffi so kake su kwana suna tari kenan."!? hannu ya d'aga masa! "Malam saurara don Allah! Kai ma sam baka da da kirki wallahi kuma daga yau nasan irin zam da zanyi da kai." Captain Habu yace."Sarkin! kishi kenan ana so ana kaiwa kasuwa ni da kake zargi ban wani kalli jikinta ba ballanta in d'arsa wani abu a raina kasan dai ba halina bane."!!! Cikin hayaniya yace."Me yasa da tazo gurinka ta zauna baka bar gurin ba sai ka zauna kana 'kare mata kallo bayan kasan yanayin suturar dake jikinta."!! Captain Habu ya saki baki kawai yana kallonsa sai surfa masa bala'i yake da ya gaji da sauraransa kawai sai ya haye katifa ya juya masa baya yana fad'in"Idan ka gaji kayi shiru ai." Haushi kamar ya kashe shi aikuwa baiyi shirun ba mita kawai yake zuciyarsa na ingizashi yabi yarinyar dakin Baba Ladidi kawai yaci ubanta....aikuwa haka akayi mikewa yayi a hankali ya fita duk sunyi bacci baba ladidi da baba marka kenan......Kai tsaye dakin Baba Ladidi ya nufa duhu sosai a dakin ya fito da wayarsa ya kunna.....Kwanciyar da tayi sai da ta kusa sumar dashi cinyoyinta duk a waje da d'uwawunta mai fad'i da tudu!! Gabansa na faduwa ya kashe hasken wayar ya nufi gadon kai tsaye ya kwanta akanta ya sauke mata nauyinsa gabad'aya kokarin birkitota yake ta bude idonta jin kamshin turaransa ya sanya gabanta faduwa "Wayy.......ai kafin ta karasa ya sanya hannunsa guda ya rufe mata baki ya birkitota bayanta a kirjinsa sai ya sanya kafafunsa ya hard'e nata 'kafafun!!! 'daya hannunsa da baya aikin komai shi ya zura cikin rigar ya d'amko kananun nonowan yana mulmulawa idan ya murza wannan sai ya murza wannan!! a maimakon Sayyada taji zafi sai ta dinga jin wani dad'i Kafin ya ankara yaga yarinya na san'kame masa a jiki tana wata iriyar mi'ka tare da sakin nishi............................. 8/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ *Free Pege15* Ganin irin abinda takeyi ne yasa yayi saurin ingijeta daga jikinsa sai ta sake ma'kaleshi tana 'kara ri'ke masa wuya, hankali a tashe ya fara lalubar wayarshi kan gadon ya samu ya dauka ya kunna haske yana kallon yanayin fuskarta sai gabanshi ya fad'i! "Yanzu kamar wannan yarinyar Sayyada har ta san wani abu."? wai tambayar kansa yake yana mamaki! Tureta yake tana 'kara shigewa jikinsa gadon 'karfe na Baba Ladidi sai 'ki!-'ki! yake Sadam! takaici ya isheshi bai san sanda ya waska mata mari ba, da sauri ta dawo hayyancinta ta bishi da kallo idanunta duk sun wani jirkici sauka yayi daga gadon yana gyara wuyan rigarsa Harara yake watsa mata yace." Banza fitinanniya kawai."! Sayyada tasa kuka tana dafe kumatun ta ashe dama ba mafarki takeyi ba da gaske ne Sadam! ne!! yake mata wasa da sassan jikinta da 'karfi tace"Bani ce fitinanniya kaina kuma Allah ya isa." Karaf! a kunnan Baba Ladidi dama bata da dogon bacci tun lokacin da gadon yake motsi ta farka to bata damu ba saboda tasan wataran Sayyada haka take da motsu-mutsu in tana bacci.....Da sauri ta kunna tochilight dinta ta mike dakyar ta kama hanyar dakin.....Dai-dai wannan lokacin shi kuma ya koma inda take yana fad'in"Don Ubanki wa kikewa Allah ya isa."? tana kuka tace"To me yasa zaka shigo dakin da daddare har ka ta'ba min jiki." Gabansa ya fad'i! cikin hantara yace."A'ina na ta'ba miki jiki sharri Shari zakiyi min ke baki da wani abu da zaki rud'e ni dashi." Ganin yana nema ya mai da ita sauna sai tace"Wallahi 'karya kake."! aikuwa ya sanya bayan hannunsa ya gwa'be mata bakinta wanda yayi dai-dai da shigowar Baba Ladidi tace",Ashsha! ashe dai masifar bata kwanta ba Sadam! me ya shigo da kai." ? Cikin rashin abin fad'a yace."Ki tambaye ta." Sai ya kama hanya zai fita. Sayyada na kuka tace"Wallahi Baba kar ki barshi ya fita bashi da gaskiya." Baba Ladidi tace."Ai naga alama ba sai kin fad'a ba, in banda jaraba me zai shigo dashi dakin nan da wannan daran." Sadam! na jinsu suna surutai ya kama hanya ya fita bai ce masu komai ba. Baba Ladidi ta kalli Sayyada duk a firgice gashin kanta duk ya tuje tace"Ki fad'a min gaskiya ko wani abu yayi miki domin ban yarda dashi ba." Tace"Babu abinda yayi min kawai ya shigo duba fulas din shayi ne wai zai sha sai nace masa ai baki dafa ba shine yake ta masifa." Baba Ladidi ta sauke ajiyar zuciya tana d'an 'kara naxarin d'akin da ita kanta Sayyadar tace"To ki kwanta sai da safe amma don Allah ki daina biye masa kuna fad'a ko kin manta aure za'ayi muku kiyi masa biyayya." Tace"To insha Allahu baba." Tare suka fito Baba Ladi ta koma shimfidarta ta kwanta ita kuma ta dauki buta ta nufi bandaki. Ko da wasa ba taji motsin mutum a ciki ba sai da ta tura sannan ta ganshi tik yana wanka Allah yasa babu haske sosai amma duk da haka taga abinda ta gani....Cikin razana ta saki 'kofar ta koma da baya tana zare ido....Kaciyarsa da ta gani a mi'ke shine abinda yayi masifar razana ta to me hakan yake nufi? ita dai tasan ba haka kaciyar maxa take ba to shi tashi ya akai take a tsaye!? babu me bata wannan amsar sai gabanta ya dinga fad'uwa cikin ranta tace"Kila bashi da lafiya ne sai kawai taji tausayinsa addua take masa Allah ya bashi lfy. Tana nan tsaye ya fito daga shi sai dogon wando da singlet fuska a daure yazo ya gifta ta ya wuce ko da wasa taki dago kanta su had'a ido..... tana ganin shigewarsa ta afka bandakin ko addua ba tayi ba....Wandonta ta cire tayi fitsari tasa hannu tana tsarki kawai sai taji tana wanko wani abu mai yau'ki ta dinga wankewa sai da ta daina jin yau'kin abun a hannunta sannan ta hakura ta fito jikinta duk a sanyaye daki ta nufa ta cire wandon ta sauya wani kana ta nemi guri ta kwanta ta rungume pillow tsananin sha'awa na damunta wanda ita takasa tantance menene da kyar bacci ya dauketa .......To shima nasa 'bangaran hakane yayi ta fama da joystick dinshi dan ta mi'ke masa sosai kawai yana tunano yanayin da ya shiga lokacin da ya had'a jiki da yarinyar taushin fatarta da yanayin yanda ta dinga narke wa a jikinsa tana mutsika shi shine abinda yake daga masa hankali dalilin kenan da ya sanya joystick din taki kwanciya haka ya dinga mirgin mirgin kan katifa yana lumshe ido gagarimar sha'awa ce ta taso masa sha'awa ta shakara da shekaru Sadam ya sha wahala a cikin daran nan kafin ya samu ya dawo norml bacci me nauyi ya dauke shi......Sai kusan shida na safe ya tashi don ba yanda Habu baiyi dashi ya tashi suje masallaci ba ya kasa tashi saboda baccin dake kansa Yana idan da sallahar ya fita suka gaisa da kawu Tanko kana ya shiga sauran 'kofofin suka gaisa da jama'a tare da yi musu sallama.....Koda ya dawo kofar su Baba ladidi sai ya tarar ta dora tukunyar kunu kan kurfoti baiyi magana ba ya dauko bokiti ya juye ruwan sai wani shan kunu yake yaje ya sanar da Habu ya fito yayi wanka a cewarsa baya so ko minti ashirin su kara a garin.....Captain Habu ya fito da shirin wanka Shi kuma ya kuma ciko tukunyar da ruwa ya dora kan wuta yaja ya tsaya had'e da rungume hannu a kirjinsa kafatanin hankalinsa na kan ruwan da ya dora kan wuta yaji motsi a bayansa....Sayyada ce ta fito da kai buyaya! da riga iya gwiwa yaji wani bala'in takaici ya kamashi dauke kai yayi daga kanta, Tana magagin bacci ta dauki buta cike da ruwa zata afka bandaki......Razananniyar tsawa! ta buga mata! sai butar ta fad'i! da sauri taja ta watsatsake! ta tsaya tana kallonsa....Ya dinga maka mata harara kafin ya ya mutsa fuska yace."Mahaukaciya me bankad'a band'aki babu tambaya to da akwai mutum a ciki." Sai tayi saurin kallon kofar 'bandakin taji motsin ruwa.....Jiki a sanyaye ta aje butar zata koma daki domin tayi bala'in jin haushin sunan da ya kirata dashi wai mahaukaciya!!! Ya dinga watsa mata wani irin kallo yana ya mutsa fuska haka ta shiga dakin Baba ladidi ita kuma ta fito da karamin bokiti cike da gasarar kunu sai ta ganshi a tsaye tace"A'a gadi aka bakane na ganka a tsaye ko da yake na manta kai yanzu ko shekara zakayi a tsaye ba damuwa zakayi ba." Shiru yayi mata tazo ta bude tukunya tana fad'in"Nasab ruwan har ya gaji da tafasa ma." Tana budewa taga kurmemen ruwa a tunkuya kuma baiyi zafin kirki ba....."Da alama dai kaine ka juye ruwan zafin nan ko."!? tafada bayan ta aje abun dake hannunta.....a dakile yace."Captain Habu na juyewa yana wanka wannan ma da kika dora ni zanyi dashi. da wuri zamu dauki hanya." Tace"To to! ko dana naji! amma dai ai ka bari ku karya tukkuna sai ku tafi daka bari an fara dama kunun." Shiru yayi mata sai ta wuce ta dauko daya kurfotin ta zuba gwayi ta hada wuta tana fad'in"Miskili kafi mahaukaci ban haushi ta inda Sulaiman yafi ka kenan." Sadam! na jinta ya share Baba marka ta fito da carbi a hannunta da alama lazimi take suka gaisa ta nemi guri ta zauna Baba Ladidi tace"Kina jina da wannan bahagon mutumin ko? Baba marka tace"Ina jinku ai naji yana yau zasu koma." Baba ladi tace"Tabbas gashinan ai a tsaye da bamu tashi da wuri ba da sai dai muga gidan wayam! sun tafi sai kace wanda ake kora." Shi dai Sadam baice komai ba Captain Habu na fitowa ya juye ruwa ya shiga wanka Captain Habu ya shirya tsaf ya fito suka gaisa dasu Baba ta zuba masa kunu mai zafi cikin jug da kosai mai zafi cikin wata samira tace "Ka karya a nutse kafin ya fito abokin naka." Tsaf! ya fito cikin milk din yadi kashmir wanda akayi masa d'in *Kufta* yadin yayi masa kyau sosai ya gyara sumar kanshi dama shi ba ma'abocin sanya hula bane yana fitowa tsakar gidan ya d'umame da kamshin turare Sadam! ma'abocin turare ne kasancewar sa mutum mara son wari ko wane iri yana da tsafta ta ban mamaki farcensa ma abin kallo farare tas tas dasu, A nutse duk ya gaishesu yanzu fuskarsa ta d'an sassauta ba kamar d'azu ba Baba Marka ta had'a masa abun kari sannan ta zubo musu farfesun su na jiya katon plate sai turiri yake tamkar yanzu akayi ta kawo masu manya manyan gurasa masu kyau da taushi.....Kunun yasha sosai bai kalli inda kosai yake ba sai ya hau yagar gurasar yana dangwala da miyar yana ci sosai girkin tsofaffin yake masa dad'i shiyasa komai zasu dafa su bashi yake ci ba tare da wani 'kyan'kya mi ba........Ta fito daga d'aki tana cika tana batsewa tayi wanka tsaf da shirin zuwa isilamiyya suka gaisa da Captain Habu a mutunce Sadam! yayi tsammanin yarinyar zata gaishe shi sai yaji shiru ransa ya 'baci ya lura Sayyada ta gama raina shi da yawa har ta gaisa da abokinsa shi ta kasa gaisawa dashi ya cika ya batse ko da wasa bai kalli inda take zaune ba tana karyawa suna hira da Habu ta saki jiki sai 'babbaka dariya takeyi...........Yana kammalawa ya mike ya shiga masaukinsu minti biyar ya fito da jakar kayansu ya kulle dakin key din ya mikawa Baba ladidi Ya kalli Captain Habu a tur'bune yace."Idan ka gama zubda girman sai ka taso mu tafi ko." ! Captain Habu ya mike yana murmushi yayiwa su Baba sallama addua suke Allah ya tsare hanya.....Sadam! ne a gaba yana tafiya sahunsa na dukan 'kasa kamar wanda zai rusa gini saboda zafin nama. shi kuwa Captain Habu sai da ya tsaya sukayi sallama tsaf da su Baba sannan ya bi bayansa. *** Sai bayan motarsu ta hau kan kwalta ne sannan ya sauke ajiyar zuciya Captain Habu ya kalleshi a nutse yace."Don Allah ka dinga sassautawa zuciyarka wani abun mana Abokina nasan akan abunda kake wannan hucin! kar ka manta da cewar yarinyar nan fa bata da waye ba irin ta mutananmu sannan akwai kuruciya a tare da ita zafin zuciya ba shine zai sanya ta dawo yanda kake so ba kai da kanka zaka dinga nusasheta ga yanda zatayi karka ina biye mata ina koya mata mu'amula ne Amma yanzu kishi ba naka bane." Wata ajiyar zuciyar ya sauke yace."Habu ina kishin yarinyar mutuka bansan meye dalili ba ko da kai naga tana magana sai raina ya 'baci! yau da ban san waye kai ba da sai na d'ora allon zargina akanka to nasan kai ba irinsu bane ba zaka tsare min mutuncina da kyau.....Aboki ina jin tsoron aje Sayyada cikin breeck dinmu yarinyar nada rawar kai sosai kuma kasan akwai ma'kiyana a gurin sannan akwai 'yan iska irinsu Shu'aibu, duk sanda na tuno hankalina na tashi mutuka."! Captain Habu yace."Kome xakayi kayi da kyakkyawar niyya insha Allahu babu abinda zai faru ai akwai masu gadi kuma nima kar ka manta nawa iyalin na ciki insha Allahu babu abinda zai faru zaka sanya ido sosai nima zan sanya ido. Allah zai tsare mana iyalinmu." Sadam! yace."Insha Allah amma kasanni kasan bani da sauki kan komai Allah duk wanda yayi gangancin shiga hurumi ranar sai dai uwarsa ta haifi wani."!!!! Captain Habu yace."Insha Allahu hakan ma ba zata faru ba." To da wannan magana ta Sadam suka rufe maganar suka shiga wata. **** Sulaiman ya dawo daga kasar hindu cike da nasarori na rayuwa, tsaraba yanda yayiwa matarsa haka yayiwa Sayyada akwati biyu cike da kananun kaya Pakistan irin na indiya da irin kayansu na kwalliya Mahaifiyarsa ya bawa akwatinan yace."Gashinan a had'a a lefen Sayyada Hajiya Fatsima taji dad'i sosai tana fatan zumuncin yaranta ya d'ore har 'yayansu da jikoki. **** Yau sauran kwana uku daurin aure.....Ya dawo gida misalin karfe shida da kwata na yamma yayi parking harabar gidan suka gaisa da mai gadi yana kallon motar Sulaiman yasan ya dawo gari, kai tsaye cikin gidan ya nufa Yana hakimce kan kujer hannunsa da katuwar waya yana latsawa fuskarsa dauke da murmushi me kyatarwa sulaiman kenan matashin da 'yan mata keso ga kudi ka kyau!!!! Sadam! yayi sallama a nutse ya tsaya daga bakin kofar ya kwance takalminsa, Sulaiman ya dago kansa yana kallonsa bai amsa sallamar ba, ya karasa babu yabo babu fallasa ya mi'ka masa hannu"Barka da yamma."! yafad'a cikin wata baud'ad'ddiyar murya wacce kana jin sautinta zaka san babu wasa a cikinta. Cikin izzah da hakimcewa ta alhazawan birni ya mi'ka masa nasa hannun "Da fatan na same ku lafiya? Ya aiki ina fatan komai lafiya."!? Hannunsa ya zare yana d'an ya mutsa fuska yace."Aiki alhamdullahi." Sai ya nemi guri ya zauna had'e da d'aure fuska tamau!! Wannan d'agawar! da girman kan! da izzar! da Sulaiman keyi na masifar bashi haushi wai shi nan me kudi ya dinga wani abu wanda shi a ganinsa wannan abun da yakeyi ba karamin hauka bane. Shiyasa duk sanda yaga yana wannan iskancin yake mugun shan kunu ya hade fuska tamau ya nuna masa shi din banza shi din wofi!!!! Sulaiman ya aje wayarsa ya kalli Sadam! da murmushi a fuskarsa yace."Lokaci nata matsowa ko? idan nayi lissafi dai-dai yau saura kwana uku daurin aure hakane ko."!? Ba tare da ya kalleshi ba yace."Tabbas! bakayi makuwa ba hakane ranar juma'a daurin aure insha Allah." Murmushi yayi ya shafa sajansa wannan sararsa ce shafa saje a kai-kai! minti biyar goma kana magana dashi sai ya shafa sajansa wannan d'abiar ma na masifar bawa Sadam! haushi sai ya dinga wani abu tamkar wani boss!!! mtsssw!!!! Yace."Wai ke don Allah me yasa bakajin shawara ne yanzu da wannan aikin naka zaka iya rike iyali? tuntuni nace kazo muyi kasuwanci ka'ki wai kai dole sai kayi aikin soja! wanda babu komai a cikinsa sai had'ari da tashin hankali kawai kaje a kasheka a banza a wof..........."Ya isa."!!!!!!! kafin ya 'karasa maganar ya katse shi a mugun fusace! ya mi'ke tsaye....Sautin muryarsa da yanda yayi maganar a zafafe shine ya fito da Hjy Fatsima daga kicin jikinta na 'bari! tace"Meke faruwa ne."!? "Wai Mama wannan guy ina ruwana dashi ne? me ya dameshi da rayuwata da abinda na za'bawa kaina ina ruwansa da iyalina ina ruwansa da aikina aikin soja na za'bawa kaina ba dan kudi ko daukaka ba ba don nayi suna ko a sanni ba na za'bi aikin soja ne domin na taimaki 'kasata ! Najeria wani gardi! 'katon banxa bai isa ya sauya min ra'ayi ba don haka Mamah tun muna shaida juna ni dashi kija masa kunne babu ruwansa dani ya ri'ke girmanshi idan ya sake ya fad'i a gurina to zan bi takai in tattaka in wuce!!!! maganar Iyalina babu ruwanka da ita meye dameka tunda banzo nace ka taimake ni ba bana fatan zuwan wannan ranar albashina ya isheni na rike matata da 'yayana Kai! kake son duniya da har kake shirya zama a cikinta kana kawatata ni duniyar ma ba a gabana take ba mtwwwws."!!!!! Yana gama maganarsa ya buga hannun kujera fuuuuuuu! ya fita dafa palon. Hajiya Fatima ta zaune kan kujera jikinta duk a sanyaye ta kalli Sulaiman da ya wani marairaice fuska tace" Meye ya had'aka da d"an uwanka shin ka manta zafin zuciyarsa ne."!? Yace."Wallahi Mama ba wani abun bane me zafi ya hasala kawai ina bashi shawara ne kin san dai saurin daukar zafi irin nashi." .Tace"Ni narasa me yasa bakwa jituwa da juna kaine babba don Allah ka cigaba da hakuri da halinsa ko bayan raina kuyi zumunci insha Allahu shima ya fara ajiye iyali zuciyarsa zata sassauta." Yace."Karki damu Mamah! insha Allahu zan cigaba da tausar zuciyata a kansa." Hjy Fatsima ta mike ta koma kicin. Suleiman shiru yayi yana tunanin abinda ya faru tsakaninsa da Sadam! girgiza kai kurrum yakeyi ransa a masifar 'bace! Ana kallo Sadam! nayi masa abinda yake so savoda tsabar kin gaskiya ace yayi hakuri shine babba to babu shakka hakurinsa ya 'kare zai dauki tsatstauran ma taki a kansa. *Tofa! Yanzu aka fara labari* 9/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ *Free Pege16* *_Na kusa gama free Pege ga duk me sha'awar cigaba da karanta book d'in to sai ya garzayo yazo ya biya kudin karatu domin jin yanda wannan bada'kala zata kaya._* *Yana* fita ya nufi sashensa watsa ruwa yayi ya fito 'kungunsa d'aure da towel kwanciya yayi kan bed dinsa tare da rintse ido yana tunanin maganganun da Sulaiman d'in yayi masa shi a ganinsa wannan ai ranin hankali ne, kan me zai sanya masa ido kan harkokinsa akan me zai dinga kushe masa aikinsa Sojoji nawa ne suka rike iyalinsu da aikin da har yake cewa ya aje aiki ya dawo kasuwanci wato yana so ya zauna a 'karkashinsa kenan! to idan ba haka ba har yaushe zai ce ya ajiye aikinsa ya dawo ya kasuwanci, aikin soja ra'ayinsa ne kamar yanda ya fad'a kuma babu wanda ya isa ya tursashi ya aje aikinsa sai dai idan mutuwa yayi, Haka yayi ta faman Juyi a kwance sai da yaji kiran sallah magariba sannan ya mike ya zura jallabiya mai karamin hannu ya sanya gajeran wando a ciki kana ya fesa turare mai kamshi ya nufu masjid. Sai bayan sallahr isha'i ya shigo gidan yana cin magani lokacin Alhaji Auwal ya dawo daga kasuwa ya bishi har inda yake suka gaisa da juna Alhaji Auwal yace "Tunda nagan ka anan nasan akwai abinda ke faruwa a brecck din naku." Yace."Kwarai kuwa Abbah aiki ake min a bangarena sunji labarin zanyi aure shine suke min gyare gyare." Alhaji auwal yace."To masha Allah ni kuwa ga shawara ." Yace."Ina jinka Abbah."Alhaji Auwal yace."Me zai hana idan an d'auro auran mun dawo Sayyada ta zauna tare damu sam! bana son zamanta a brecck din nan wallahi." Ajiyar zuciya ya sauke a hankali yace."Nagode Abbah nima na dad'e ina wannan tunanin to kawai bana son in takura muku ne yasa na amince da zamanta a brecck din." Alhji Auwal yace."Kana bani mamaki! Sadam! shin wai su waye iyayenka."!? Yace."Kune Abbah." "To meyasa kake janye jikinka damu ? yanzu dan kazo kace Sayyada ta zauna tare damu sai mu hana kar ka manta fa da cewar dani da mahaifiyar yariyar uwa daya uba daya muke ko babu aure a tsakaninku ni me riketa ne." Yace."Kwarai kuwa Abbah." Alhaji Auwal yace."To don Allah ka daina wannan d'abi'ar taka." Yace."Ayi hakuri Abbah insha Allah." Hajiya Fatsima ce ta fito daga d'aki tana jan akwati ta aje ta dauko dayar tace"Sadam! wannan akwatin d'an uwanka ne ya kawo maka da duk kayan dake ciki yace a had'a a lefe." Kici-kici yayi da fuska yayi shiru! tace"Naga ka 'bata rai kai bakace komai ba sai hidima ake maka kana kwance."! Yace."To Mamah me zance." Tace"kace ka gode sannan don Allah ka rage zafin rai ka zauna da kowa lafiya d'an uwanka na son ku zauna lafiya amma kai kullum cikin fushi da d'acin rai wannan ba sara bace." Yace."To Mamah! na daina isha Allah." Yasan in ba haka yayi ba to zata dinga nanata maganar ne. Tace"To ka bude kayan ka kalla yace."to duk dan ya faranta mata rai ya bude akwatinan yana dubawa kayane na gani na fada masu masifar tsada sarkoki abubuwan hannu dogwayen riguna dasu pakistan turarrika masu kamshi da tsada.....Sai Uban 'kananun kayan bacci masu kyau.....Sam hankalinsa bai kwanta da kayan ba don ba yarda zaiyi ne ya rufe akwatinan yace."Kaya sunyi Mamah." Tace"To ko kaifa gobe zamu tafi can *Dabin* zamu tafi da akwatinan lefan su gani in yaso sai a dawo dasu. yace."Hakan yayi kyau." To hira ce ta 'barke a tsakaninsu, Sadam! na fad'a musu banan babu wata uku zasuyi tafiya zuwa wani 'kauyen 'kayau dake can cikin Maiduguri domin kwantar da tarzomar da take tashi a yanki wanda masana bunkice sukayi itifakin cewa 'yan boko haram din da suke cikin wannan yanki suna da yawa kuma mafiya akasari sune suke sajewa da mutane su fito cikin gari da cikin kasuwanci suyi aika-aika su gudu kuma neman duniya ba'a ganinsu duk kuwa sojan da yayi gangancin shiga wannan kyauye to sunansa matacce, sai mai tsananin rabo ne yake dawowa da ransa amma fa sai yayi jinya me tsayi domin sai sun rautana shi. Daga jin yanda yake basu labarin had'arin dake cikin 'kauyan sai duk jikinsu yayi sanyi Hajiya Fatsima tace"Sadam! daka hakura da zuwa wannan gari jikina har yayi sanyi da jin wannan magana." murmushi yayi yace."Mamah mutukar kikaga banje wannan jihadin ba to bana numfashi a doran duniya ke dai addua kawai zaki cigaba da yi min." Tace."To Ubangiji Allah ya baku nasara ya kuma dawo mana daku lafiya."Alhaji Auwal dashi Sadam! din suka amsa da "Ameeen Ya rabbi."! *** Amarya Sayyada fa sai gyara take sha ta ko wanne fanni domin can 'bangaran mahaifinta ma kullum sai sun kirata sun turara mata jiki da had'in turare sannan sunyi mata dame-dame na maganin gyara tasha sun shafe ta da lalle tare da bata rubutu na tsari a cewarsu wannan lokacin ne ya kamata su nuna mata kaunar da suke mata, Mahaifinta yayi mata siye-siye sannan ya bata shanu biyu saniya da sa yace amma za'a ajiye mata a garin duk zuriar da ta samu nata ne Sayyada taji dadin kyautar da mahaifinta yayi mata Kakanta maigari ma yayi mata kyauta ta ban mamaki! kowa ya kula da Sayyada a cikin gidan Maigari banda matar babanta Allah ya sanya alkairi ma ta kasa cewa saboda tsabar bakin cikin dake damunta *Wannan kenan* Cikin 'yan kwanakin da Sayyada tayi tana shan magani gami da kar'bar gyaran jiki sai ta ciko sosai tayi kwarjini kyawunta ya sake fitowa fatar jikinta ta goge sosai ta zama abin sha'awa in ka ganta sai ka rantse da cewar cikin birni akayi mata gyaran amare saboda yanda ta koma, Kullum tana gidan Mariya tare da Ummi da sauran kawayen su suna shirya yanda al'amarin biki zai kasance.....Amina ta 'karfi da yaji ta shiga cikinsu ta saki jikinta ana hidima da ita tun suna zaginta suna mata dariya har suka kyaleta domin ta kiyin zuciya.....Ummi ce ta yankawa Sayyada salatif mai tsari da burgewa suka hada lalle yanda zaiyi kyau yayi kamu! aikuwa Sayyada ta fito ras da ita jan lallan yayi masifar kyau abinka da farar fata. Kitsone Sayyada tace bata so saboda tsan ko anyi ba zaiyi wani tasiri ba, sai Mariya ta dinga tsokanarta tana fadin ai gwara ki kitse kanki wallahi don kin san kullum sai ya jike da ruwan wanka." Dariya suka sheke da ita suka tafa Sayyada tace"Ke nifa yanzu na fara jin tsoro wallahi."Mariya tace."Duk tsoranki baki kaini ba gashi ni na hakura na zama 'yar gari." Haka suka 'bata lokaci suna hira kafin suyi sallama da Mariya su nufo gida. **** Yau Juma'a uku ga watan bakwai shekara ta dubu biyu da bakwai aka daura auran Sadam! da Sayyada, Kan sadaki dubu hamsin wanda Sulaiman ya bada da aljihunsa wannan al'amari yayi masifar 'batawa Sadam! rai da kansa ya bada sadakin auran sa naira dubu talatin amma saboda tsabar son a sani yayi gaggawar mi'ka nasa sam bai wani burgeshi ba ya fi son komai yayi da kansa tunda har ya fara goranta masa kan aikinsa to baya so ya gaza ta ko wanne fanni. Labarin daurin auran na isa cikin gidan Sayyada jikinta yai 'kwata'kes! salo-salo taje ta kwanta kan gado gabanta na fad'uwa! gayyar 'kawayenta ne da suka zo suka sanya ta saki jikinta duk sunci kwalliya dai-dai gwargwado amma kuma kana ganinsu zaka gane akwai banbaci da 'yan cikin gari......Itama amaryar tana sanye da Swiss les purple anyi mata dinki stone work dake duk Hjy Fatsima ta bayar an dinka mata rabin kayan lefan dinki irin na 'yan birni Sayyada tayi kyau sosai ta gyara gashinta ya sauka gadon bayanta ta yafa dankwalin les din kana sanya takalmi plete da pose irin ta amare tayi kyau sosai sai dai kana kallonta zaka gane bambamci da ita da amaryar cikin gari sannan kuma akwai yarinta a tare da ita tunda yanzu ba tafi shekaru goma sha hudu zuwa sha biyar ba........Jama'ar da suka cika gidan suka dinga janta da wasa tana dai daurewa tana gaishesu da abun yayi yawa kawai sai ta fashe da kuka ta rungume Baba Ladidi to itama Baban ashe 'boye kukan take ganin Sayyada nayi sai itama ta fara nata aka rasa me basu hakuri su hakura....Cikin wannan hali suka shigo gidan....Sadam! da Sulaiman kaya iri daya ne a jikinsu shadda ce galila dinkin babbar riga, Sulaiman fuskarsa a sake ya dinga gaisawa da jama'a shi kuwa gogan bai wani tsaya sosai ba a gurin tunda yaga abinda yake faruwa takaici yasa ya bude dakin da suke sauka ya shige har da turo kofa....Sulaiman kam wayarsa ya fito da ita ya dinga musu hoto yana dariya sai da yaga abun nasu yana nema yayi yawa sannan ya soma rarrashinsu da kyar suka daina kukan Jama'a kuwa sai dariya ake musu. Yana daga kwance cikin dakin yana jiyo abinda yake faruwa juyi kawai yake yana mamakin zubar da girma irin na Sulaiman yana jiyo muryarsa yana tsokanar Sayyada ji yake kamar ya tashi yaje ya kwad'e shi don takaici......."Yaya Sulaiman bamu wayarka muyi selfie." muryarta ya jiyo cikin taratsi tana wannan maganar.....Kafin ya ankara yaji sulaiman din na cewa"Muje inyi muku keda 'kawayen naki." Firgigt! ya mi'ke zaune rigarsa da ya cire ya dauka ya sanya ko botiran bai mayar ba ya fito fit!!! ai tuni sun fice daga gidan.....Kai tsaye hanyar fita ya nufa, yana jin yan biki na fad'in"Ango kasha kamshi Allah ya sanya alkairi." bai ce komai ba yayi gaba........Can baban soro ya riskesu suna ta hauka shi kuma Sulaiman din sai biye musu yake yana dariya harda Mariya da take matar aure ta cire mayafi tana gantsare-gantsare wai ita dole hoto takeyi tana so tayi kyau........."Wannan wane irin hauka ne."!!!! muryarsa ta sanya suka juyo da sauri....yana tsaye da fuska a daure ya hard'e hannunwa a kirji yana watsa musu dan iskan kallo....Ya kalli Sulaiman cikin takaici yace."Wannan dai ba girman ka bane wallahi karfa ka manta da cewar wa d'an nan yaran ba irin 'yan matan cikin gari bane babu abinda suka sani bayan haka kuma akwai matata a cikinsu dai-dai kenan kazo kana daukarsu a hoto kana dariya." Sulaiman yayi shiru ransa ya 'baci Sadam bashi da mutumci kuma baya jin kunyar ya tozarta shi a gaban ko waye.....Ba tare da yace masa komai ba ya wuce ya barsu a gurin.....Cikin tsawa! yace."Dallah! malamai ku wuce ku bawa mutane guri in banda hauka kawai kun tsaya gaban gardi irin wannan yana muku hoto wai ku kyawawa! mtsssw!!!! Su Mariya suka shige cikin gidan jikinsu duk a sanyaye Sayyada taji haushin wulakancin da yayiwa kawayenta sai ta dinga zumbura baki tana hararasa! tazo zata wuce yace."Dube ta sam bata dace da amarya ba."! "To ai kai ma baka dace da ango ba." Yace."Ke waye ya fad'a miki dama ni ango ne."!? Hararsa tayi yace."Ni kike harara mara kunya." Ta juya tare da fad'in"Duk inda ango yake yana farin ciki amma banda kai kowa yace ka sanja hali ka'ki ji! Ni ba zaka takura min da kawayena ba tunda ai ba da wayarka muke hotonba." Yace "Zo nan ki 'karbi wayar tawa kuje kuyi hoton." Cikin rashin wayo ta dawo shi kuma ya zura hannu kamar zai dauko wayar caraf! ya rike damtsenta! suka kalli juna ita dashi saurin dauke kansa yayi jin wani irin maganad'isu na fizgarsa zuwa gareta....Cikin kasalalliyar murya tace"Sakar min damtse."! "Idan na'ki fa."? yafad'a cikin wani irin voice hucin numfashinsu ne yake had'uwa sai jikinta ya soma kyarma! shi kuma ya kurawa bakinta ido yana kallo a hankali yace." Su Sayyada amarya." Dauke kanta tayi tana shan kunu. Ya saki murmushi tare da cizan lipls dinsa na kasa yace."Ina fatan kin shirya kar'bar angon naki." Zumbura baki tayi tana dauke kai! murmushi yayi ya sakar mata hannu yace."Ki shirya da kyau! ni ba ragon namiji bane kuma bazan d'aga miki 'kafa ba." Murguda baki tayi tace"Ai a shirye nake kuma waye ya fad'a maka nima raguwa ce."!? ido ya zare ya bude baki yana kallonta cike da mamaki! fari tayi masa da gadar-gadar din idanunta wanda yasa ya kusa faduwa a gurin ta juya ta shige cikin gidan......''Iyeee! ashe dai 'yan matan 'kauye suna da abun mamaki yanzu ya tabbatar da cewar Sayyada tasan aure tasan abinda akeyi a zaman aure, lallai akwai badakala kenan.....Shifa baya jin zai taki yarinyar a yanzu sai ta zama cikakkiyar mace a ganinsa a sannan ne zata iya d'auke masa dukanin bukatarsa a yanzu yana ganin idan ya kusanci yarinyar zai iya sanyawa ta had'u da yoyon fitsari tunda yawanci masu irin shekarunta ke haduwa da lalurar ya girmi Sayyada da kusan shekaru ashirin kuma karfinsu ba daya bane jarabarsu ba daya bace shiyasa kawai ya yanke shawarar bari ta kara shekuru sai suyi zaman aure mai tsafta Sayyada na shiga cikin gidan suka ke'be da Mariya tace"Mariya kinji abinda yake cewa kuwa."? Mariya tace"Sai kin fad'a." "Humm! wai cewa yake yi dafatan na shirya masa kaina ni wallahi tsoro nake ji fa." Mariya ta dinga dariya tace"Ke mijikin wayayye ne don Allah ki saki jiki kusha soyayya." Sayyada tace"Mariya kenan baki ga abinda na gani bane shiyasa kike cewa in kwantar da hankalina." Sayyada duk sanda ta tuno da sandar girman Sadam! sai gabanta ya fad'i! domin ba zata ta'ba mance ranar bankadashi a bandaki ba." To haka aka cigaba da gudanar da sha'anin biki da al'adar garin....Kwana uku bayan daurin aure suka shirya tafiya Sayyada ta cika gidan da kuka tana kukan rabuwa da Baba Ladi baba marka suma kukan suke da kyar dai aka taushe ta tayi shiru aka kaita can gidan iyayenta nan ma sai da tayi kuka sun jima da mahaifinta nayi mata nasiha hakanan maigari ma yayi mata nasiha da fatan zaman lafiya sannan sukayi sallama da juna. ***** Biyu shaura na rana sun isa garin Kaduna garin gwamna Nan ma jama'a ce cike da gidan 'yan uwan hajiya Fatsima da makota da abokanan arziki sai hidima sukeyi Ango da Amarya na shigowa suka cika gidan da bud'a suna tsokanar Sadam! sai sannan taji muryarsa yana ramawa harda dariya....'yar autar su Hjy Fatsima ce mai suna Zuhura ita ta ja hannun Sayyada suka shige can bedroom dinta ta bude mata lullubin sayyada ta dinga jin kunya tana kauda kai sai da taga zuhuran ba wata babba bace sai ta saki jikinta suna hira haka 'yan uwan hjy fatsima suka dinga shigowa d'aya bayan d'aya suna ganinta tare da sanya albarka Sadam! na kowa ne shiyasa suke kaunar matarsa. Aunty Luba ce ta shigo tana cire 'kafa d'akyar kana kallonta kasan ta kusa haihuwa tazo ta rungume Sayyada tana fad'in"Sannu da zuwa amaryamu." Sayyada na jin muryar aunt Luba ta bude mayafi rungumeta tayi tace"ashe baki haihu ba." Luba tace"Ina kan hanya Sayyada ku tayamu addua." Tace."Insha Allahu aunty.....Tare suka ci abinci suna hirar yaushe gamo sayyada ta sake da ita sosai dama tuntuni sun saba tunda Sulaiman na kaita *Dabi* tun kafin auransu sannan duk sanda yaje *Dabi* yana bata waya su gaisa shiyasa sukayi sabo da juna. Anan ne take jin labarin tafiyar Sulaiman din bayan daurin aure tafiya ta kamashi 'kasar larabawa *Qatar* sati biyu zaiyi ya dawo....Sayyada tayi masa fatan alkairi da dawowa lafiya. *** Sai misalin karfe takwas na dare sannan gidan ya samu sau'ki masu aiki sun gyara ko ina na gidan kowa kuma ya kama gabanshi sai aunty Luba wacce dama tun bayan tafiyar mijin nata ta dawo gidan sai ya dawo tukkuna Hajiya Fatsima tace"Da zuhura ta zauna ta d'ebe mata kewa tunda anyi hutu......Hajiya Fatsima ta shigo dakin ta tarar dasu suna hira ta kalli Luba tace"Ya kamata Sayyada ta shirya sai ku rakata dakin mijinta ko."? aunt luba tace"To Mamah! tana fita Luba tasa Sayyada tayi wanka tas ta gyara mata jikinta kana ta feshe mata jiki da turare masu sanyin kamshi ta bata wani material mai kyau da tsada tasa ta yafa mata mayafi kalar material din takalmi sabo ta sanya suka fito a tare Hajiya Fatsima tayi mata nasiha sosai dangane da zaman aure.........Kai tsaye bangaran Sadam! din suka nufa lokacin yana daf da fitowa sai sukayi kici'bus! fuska ya saki sosai suka gaisa da Luba duk fad'an da sukeyi da Sulaiman bai shafeta ba saboda yana ganin mutuncinta sosai matace mai hankali da aiki da iliminta yace."Da kin bari ma nazo na dauki amaryarta da kaina ai ba wani abun bane." Tace"Oho dai naji ai komai zaka fada sai dai ka fad'a ni bana kishi tunda dai nasan nice uwar gida." Yace."Ai kuwa yanzu na daina yayinki tunda na samu amarya." Dariya tayi tace"Ai dama wannan halinku ne." hanya ya basu suka shige yace."To ni dama fita zanyi amma ba zan dade ba." Hararasa tayi tace"Kana da amaryar zaka fita yawo ko aiki ne da kai ya kamata ka dauki Uziri." Yace."Karki damu yanzu zan dawo insha Allah....Gurin aiki zan nufa yanzu amma bazan wani dade ba tunda nasan akwai amarya ke dai kawai ki zauna kiyi min gadinta." Tace."Baka isa ba nima ka barni da kishin dake damuna." Dariya ya dinga 'kyakyatawa ya kama hanya ya fita....Sayyada ta dinga mamakinsa dama haka yake sai dariya yake har da kyakyawata lallai ma Yaya Sadam! ita sai yayi ta sha mata kunu yana mata tsaawa. Aunty Luba ta d'an zauna mata amma da taga dare yayi sosai sai tayi mata sallama ta koma can sashen su Hajiya......Sayyada tayi tsuru kamar mayya motsi kadan ta duba agogo karfe goma sha biyu da rabi tayi bai shigo ba sai ta kwanta kan gadonsa tana kuka haka bacci ya dauketa bata tashi ba sai asubah!!! tana kokarin sauka daga gadon ne taji motsin shigowa cikin palon ta koma ta kwanta nan taji ya turo kofar dakin ya shigo ya jima tsaye a kanta yana kallo duk a tunaninsa bacci take yaje yana jan kafafunta" Taki bude ido mugun haushinsa takeji ta dauka zaiyi ta rawar kai a kanta kamar yanda angwaye keyi shi sai yayi wanka ma yayi ficewarsa saboda bata da matsayi a gurinsa.....Da ta gaji da jan kafar ta da yake sai ta fuzge da karfi ta jiyo muryarsa yana fadin"Tashi kiyi sallah." Toilet ya nufa ta bishi da harara! Taji ciwon abinda yayi mata ya nuna bai damu da ita ba shiyasa yaje ya kwana a waje....jin motsin bude kofa yasa ta dauke kanta da sauri ya fito ya sauya jallabiya duk tana kallonsa ya dauki carbi ya fita....Nan ta mike ta nufi bandakin domin daura alwala. 10/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ _*Na kusa gama free peges duk mai bukatar cigaba da karanta littafin sai ta garzayo ta biya kudin kararu*_ *Free Pege17* Wanke bakinta tayi da brush sannan ta daura alwala ta fito ta shimfida dadduma hijab ta zura ta tayar da sallah ta jima tana addua kafin ta kwanta bacci me nauyi ya dauketa.....Sai da gari ya fara haske sannan ya shigo gidan....Ganin tana bacci yasa ya tsallaketa ya nufi toilet din yayi uzurinsa ya fito kan bed ya nufa ya kwanta rigingine yana kallon rufin dakin bacci yake sonyi yaji motsinta idanunta da alamun bacci take kokarin hawa bed din da sauri yaja gefe yana kallonta taja bargo ta rufe kafafunta da alama bacci takeji sosai. Fuskarta ya tsurawa ido yana kallo Yarinyar tana da kyau sai da tayi 'kankanta wata zuciyar tace masa sau nawa ana yiwa yara aure irinta kuma su zauna lafiya har kaga an haihu....."Tabbas hakane " yafada a ranshi to ammafa shi duk da haka yana jin tsoron haikewa yarinyar kar yaje ya had'ata da wata lalurar shiyasa yake so tayi 'kwari tukkuna.....Le'bunanta ya tsurawa ido yana kallonsu cike da sha'awa wai yanzu wannsn 'yar ficiciyar itace matarsa wanda yana gani da wata babbar macen ce da tuni ya kawar da kwadayinsa na shekara da shekaru. Bacci takeyi sosai amma duk ta matso jikinsa tana nani'karsa, shi kuma sai matsawa yake yana ture ta, tana sake matsowa tsawa! ya buga mata"Ke! meye hakane."!? ta bude idonta dake cike da bacci.... ganin idanunta a lumshe ya sanya duk wata sha'awarshi ta tashi yayi saurin mikewa zaune yana hararata"Idan ba bacci xakiyi ba to ki saurara haba! mutum da dakinsa anzo an hanashi ya huta." Turo baki tayi gaba ya dauke kansa tare da jan karamin tsaki ya koma ya kwanta yana kallon cilling shi kadai yasan abinda yake damunsa mamaki yake wai yarinya kankanuwa tana nema ta burkita masa lissafi ko Halima da take cikkakiyar mace bata ya mutsa masa lisaafi ba sai wannan yar k'ank'anuwar. Sayyada na sani ta dinga matsawa har sai da ta dangane da inda yake ta d'ora kanta a kirjinsa ta cigaba da lumshe idonta takaici da 'bacin rai suka dameshi ya lura yarinyar fitinanniya ce kuma bata jin tsoro yanzu a wannan zamanin yarinya 'kan'kanuwa kamar sayyada har ta san ta kai kanta gurin miji......kyaleta yayi kawai kanta a kirjinsa haka bacci ya daukeshi sai da taji saukar numfashinsa sannan ta bude idonta ta tsira masa ido tana kallo Allah da ya hallice ta ya zuba mata 'kaunar Sadam! tana fatan tayi rayuwa mai tsayi tare dashi sannan tana addua Allah yasa ya sota kamar yanda take sonsa.....Bacci gagararta yayi ta lalace gurin kallonsa sai da ta gaji don kanta sannan ta mike taje tayo wanka ta shirya jikinta tsaf turarasa masu tsada ta dauka duk ta feshe a jikinta mayafi ta yafa ta sanya takalmi plate ta nufi bangaran su Hajiya. Hajiya Fatsima na kicin ita da mai aikinta suna aikin break fast ta shiga palon ta zauna Hjy Fatsima ta fito daga kicin ta ganta a zaune sakin fuska tayi sosai Sayyada ta sakko har 'kasa ta gaisheta Hjy Fatsima ta amsa a sake tana tambayar ta gajiyar biki.Murmushi kawai tayi. Aunt Luba ce ta fito da shirin zuwa asibiti ta zauna kan kujera suka gaisa Sayyada tace."Aunty Luba da muje in raka ki asibitin ko." Tace"Karki damu Sayyada Sulaiman ne zai zo. yanzu ya daukeni." Tace."To aunty bari in kar'bo miki break fast kiyi ko." Aunty Luba tace"Nagode kanwata." Tare sukayi bresk fast din aunty luba na tsokanarta amarci ita dai ba tace komai sai dariya kawai take. Sulaiman ne ya shigo cikin kananun kaya yayi kyau sosai hannunsa rike da key na mota, Sayyada sai fara'a take yi "Yaya Sulaiman sannu." ya zauna kusa da ita yana amsawa tare da fadin"Ina angon naki."? hannu tasa ta rufe fuska murmushi yayi yana danne 'bacin ran dake taso masa. Hajiya Fatsima ta fito daga kicin ganin Sulaiman a zaune sai ya bata mamaki tace"Yaushe ka dawo gari."? Yace."Jiya na shigo da daddare munyi waya da Luba ashe bata fada miki ba." Luba tace"Mamah naga dare ne shiyasa ban sanar dake ba." Hjy Fatsima ta zauna suna gaisawa yace."Luba tayi min waya da safe wai bata jin dadi dole sai taje asibiti." Hjy Fatsima tace"To in banda abinka mace me tsohon ciki kamar wannan yaushe zaka sameta da lafiya." Yace."Allah dai ya raba lafiya."Ameeen suka ce gabad'aya. A gurguje suka kammala karin kummalon sannsn suka wuce asibitin Sayyada ta gyara gurin ta koma ta zauna Hjy Fatsima tace"To ai sai ki had'a kayan karin ki kaiwa mijin naki ko Sayyada." Tace."Ai bacci yake."Tace"Eh ki had'a komai ki kai masa kinga idan ya tashi sai ya gani." Tace"To Mamah." Kicin ta shiga ta hada komai cikn kwando ta dauka ta nufi bangaran nasu. Koda ta shiga dakin har yanzu bacci yake ya rungume pillow 'kam! ya sanya wani a tsakiyar 'kafafunsa daga ni baccin a takure yakeyinsa.....Kwandon ta aje ta matsa jikin bed din tana jan pillows din ya ri'ke 'kam! yana sauke ajiyar zuciya......"Yaya Sadam!!!! Yaji muryarta ta daki dodon kunnensa firgigit ya mike zaune yana kallonta da jajayen idanunsa wanda suke dauke da tsabar fitina mafarki yake gashi yana sex da ita yana jin wani irin nishadi wanda har yake mamaki ashe zai iya samun gamsuwar da yake so da ita. Ita kuma ganin yanda kwayar idonsa ta sauya sai taji tsoro ta dauke kanta da sauri.....A hard'e! yace."Waye yace kizo ki tashe ni ina baccina mai dad'i!!!! Tace."Mamah ce tace in zo in tasheka ka karya." Yace."karya kike mamah tasan ba'a tashina idan ina bacci." Sai ta d'auke kai tana turo bakinta wannan d'abi'ar tace zu'baro baki......Girgiza kai yayi yace."Wuce ki bawa mutane guri." Matsawa tayi ta jingina da bango(garu) "Cewa nayi ki fita a dakin malama." 'Kin fita tayi ya dinga magana tana jinsa tayi shiru dalilin da yasa baya so ya tashi a gabanta saboda yasan sandar girmansa a mi'ke take shiyasa baya so ta gani ya lura yarinyar 'yar bin 'kwakkwafi ce......Yace."Bakiji abinda nace ba ko."!? "To wai me na tsare maka ne ga hanya nan fa na baka ka wuce dole sai kace sai na fita daga dakin."!! 'Kwafa yayi ya yunkura ya mike!!! aikuwa karaf! idanunta ya sauka kan abinda yake 'boyewa, hannu tasa ta toshe bakinta sai kace wacce taga gagarimin abu........Sai ta dauke kanta tana d'an kumshe dariya Takaici tamkar ya kasheshi wai shi wannan yarinyar takewa rashin mutunci ko da yake to me zai 'boyewa sayyada dama ta riga ta gama ganin girmansa......Yana daf da shiga toilet din ne ya jiyo muryarta tana fad'in" Gaskiya Yaya Sadam! ka nemi magani baka da lafiya ta'b!!!!!!."""" bai ce mata komai ba ya shige amma ya cika da mamakin jin furucinta wato shine ma bashi da lafiya kenan aikuwa sai yaci ubanta zai nuna mata garau! yake zata gane shayi ruwa ne.....Wanka yayi ya fito fuskarsa a daure tamau!! tana ta kallon fuskar tana kumshe baki.....Ya mutsika basilin turare ya fesa ya kawo sabuwar jallabiya yasa still yana jiyowa yaga tana masa dariya hade da gumtse baki......Cikin fusata yayo kanta da gudu ta ruga palon tana kyakyatawa......Ya tsaya tsakiyar dakin hade da rike kugu yana mamaki! gyada kansa yayi ya koma ya zauna kasan kafet da kansa ta hada abincin yaci ya koshi ya ture kwanikan kana ya mike domin gaida iyayensa. Koda ya isa bangaran iyayen nasa abin da ya gani ya 'bata masa rai Sayyada da Sulaiman kujera d'aya 2sitar suna zaune suna hira ita kuma Luba na kwance tsakiyar kafet tana kallonsu jefi jefi tana sa musu baki....Da kyar ya daure ya isa inda suke hannu ya mi'kawa Sulaiman d'in suka gaisa babu yabo babu fallasa, ya zare hannunsa tare da watsa mata wani irin kallo....Jikinta ne yayi sanyi sai ta rage dariyar da takeyi ta shiga hankalinta.... Dakin mahaifiyar tasu ya nufa suka gaisa sai ya lura da ita kamar bata son su hada ido don haka bai ja wata doguwar magana ba ya fito.....Ba tare da ya kalli inda suke ba ya kama hanyar fita yana ji Luba na masa wasa bai tanka mata ba mugun haushin mijinta yake ya rasa gane me yake damun Sulaiman son matansa yayi idan da yana daukar Sayyada 'yar uwarsa to yanzu kuma da take auransu ai ya kamata ya kama kansa tunda yanzu kamar a matsayin suruka take a gurinsa. amma saboda tsabar zubar da girma ya zage yana dariya da ita.........Harabar gidan ya zauna gurin hutawa yana duba sa'kwanni abokanshi, Captain Habu ya kira shi a waya cewar ya fito yanzu yanzu yanzu labari ya same su cewar an samu wani d'an boko haram! ya shigo kasuwar bacci kuma ana zargin anan ya kwana cikin tasha." Daga jin wannan magana sai yayi zumbur ya mike bangaransa ya nifa domin shiryawa....Tsaf ya shirya jikinsa da kayansu na sojoji ya fito, Sayyada na ganinsa cikin kayan aiki sai gabanta ya fad'i! Sulaiman yace."Ya dai naga kayi shirin fita aiki kai ko d'an hutun amarcin ma baka dauka ba." Wani irin kallo ya watsa masa kamar ya gargad'e shi sai kuma ya fasa. Hajiya Fatsima tace"Da'alama aikine ya tashi yanzu." Yace."Eh mamah nan ya zauna ya fada mata halin da ake ciki.....Sayyada dajin wannan magana sai ta fashe da kuka"Yaya Sadam! don Allah kar kaje kar su kashe ka."!! Palon yayi shiru.....Aunty luba tace."Wallahi nima jikina yayi sanyi Sadam! ya mike da fad'in"Addua kawai zaku dinga yi mana." Ganin ya nufi hanyar fita ya sanya sayyada ta ruga a guje ta rungumeshi ta baya tana kuka........Wannan lokacin Sulaiman ji yayi tamkar ya harbe Sadam! saboda kawai sayyada ta rungume shi wai shin shi me Sadam! yafi shine ? da Sayyada take sonsa, hakika yana jin bala'in ciwo a cikin zuciyarsa son da yakewa Sayyada yayi yawa kuma yanzu ya tabbatar da cewar tayi masa nisa tunda ta kasance matar 'kaninsa. Kuka takeyi sosai! har sai da ta bashi tausayi yaja hannunta suka fita motarsa ya nufa da ita ya bude suka shiga"Goge hawayen ki."Ya fada tare da mika mata hankici mai kamshi Bayan ta goge sai ya mika hannu ta bashi makale kafad'ata tayi yace."Saboda me."? "Saboda ina son 'kamshinka Don Allah Yaya Sadam! kar kaje gurin nan kaji ina sonka bana so wani abu ya sameka."! Ajiyar zuciya ya sauke a hankali yace." Kin gane ko Sayyada shi wannan aikin namu daban yake da sauran, muna taimako da tsare rayuka da dukiyoyin talakawa ne kuma kafin mu kar'bi aikin sai da mukayi rantsuwa da al'kawari kan cewar komai wuya rana zafi ruwa sanyi zamu fito a duk lokacin da wata tarzoma ta tashi zamu taimaka koda zamu rasa ranmu saboda haka ki kwantar da hankalinki babu abunda zai sameni sai alkairi." Hawaye take tace"To Ina rokon Allah ya tsareka kuma ya baka nasara mijina." Murmushi yayi irin wanda bai ta'ba yi mata irinsa ba ya "karbi hankicin ya goge mata hawaye kana ya mika mata ta kar'ba tana murmushi.....Shina murmushin yake yana kallon fuskarta. Hannu yasa ya d'ago fuskarta a hankali yace." Bani nasha."! ta lumshe idonta tare da budewa sai taga fuskarsa daf da tata, rintse ido tayi gabanta na fad'uwa.....Murmushi ya saki ya sakar mata fuskar ba tare da yayi mata komai ba yace."Kije gida kiyi min addua amaryata." Ta bude kasalallun idanunta tana kallonsa hannu ya zura ya bude mata kofar motar ta fito ya daga mata hannu kana yaja motar mai gadi ya bude gate ta figi motar a guje ya fice!!! ta jima a tsaye a gurin tana kallon hanyar da ya wuce jiki a mace ta koma bangaransu ta kwanta inda ya kwanta jiya ta dauki jallabiyarsa da ya cire ta rungume a kirjinta tana hawaye. haka bacci ya dauketa. Sulaiman kuwa ganin Sayyada bata dawo ba sai yaji duk xaman gurin ya isheshi tashi yayi zai fita aunty Luba tace"Darling yaushe xamu koma gida ne.? ba tare da ya juyo ba yace."Duk sanda kika shirya komawa." Ta mike da kyar tana fadin "Yanzu ma a shirye nake." Tsaki yaja ya fita sai ta bishi da kallo cike da mamaki! auran soyayya sukayi da juna amma tunda ta samu ciki ta rasa gane kansa da gidinsa wulakancin yau daban na gobe daban, kwata-kwata bashi da lokacinta sai aukin hira da 'yan mata a waya. Ta wagar sojojin na shiga cikin kasuwar jama'a suka soma watse masu sana'a da suka karkasa kayansu suka soma kwashewa Sadam! ya kar'bi abin 'kara karfin murya yace."Kowa ya zauna ya nutse kuma ku daina kwashe kayan sana'ar ku bunkice muka shigo zamu tafi idan mun gama mu barku ku cigaba da sana'oinku.'' To sai da sukaji wannan magana sannan hankalinsu ya kwanta....Su kuma sojojin sai suka watsu dana already wasu sun rufe gate din gaba da baya kuma tsun tsare hanya......Sadam! ya dinga kutsawa cikin rumfunan jama'a ya duddubawa su kuma sauran suna zazzage buhunhuna! na kayayyakin sana'a duk wasu daurarrun kayan sai da suka kwance suna dubawa babu wata alamar ganin mutum......duk fad'in kasuwar sai da suka bunkita basu ganshi ba....Sadam! ya ri'ke 'kugu yana kallon tarin jama'ar da sukayi tsuru-tsuru suna jimami d'an boko haram! ya shigo cikinsu basu sani ba wasu daga cikin ma har sunyi alkawarin cewa daga yau ba zasu sake fitowa kasuwa ba har sau gwamnati ta shiga al'amarin......Dai-dai inda yake tsaye karkashin wata katuwar kwata ce da aka rufe ta da silaf kwatar tun daga farkon kasuwar take har karshenta kuma duk rufe take da Silaf.....Babu zato! Sadam!! yayi 'yar hantsle!!! Ya ganganra can! gefe kafin kice kwabo guri ya hautsine da hayaniya kowa naso ya tsira da ransa......Cikin zafin nama ya mi'ke.....da gudu! ya nufi gurin kafin ya 'karasa an jefo wani abu!!! jama'a na dubawa suka ga bomb!!!!! Sai ihu! gudu karce! marasa karfi sai faduwa sukeyi ana tattake su kowa dai na neman ya ceci ransa.......Ba tare da wani tunani ba ya afka cikin kwatar, Can ya hango shi yana gudu!!! cikin kwatar bakajin komai sai motsin ruwa!!!! Sa'ilin da gurin ya hargitse ne aka samu wani wanda yayi saurin mayar da silaf d'in da wannan d'an boko haram d'in ya cire ya rufe gurin alhalin yasan Sadam! na ciki......Jama'a sunyu dafifi bakin gate suna ihu! ga gate a kulle marasa hakuri kuwa ai har sun soma haura katanga suna dura 'kasa, Captain Habu ne yazo cijn zafin nama ya bude gate din aikuwa jama'a suka dinga turareniyar fita......Captain Aminu shine yayi jihadi ya d'auki bomb din a guje ya fita dashi can cikin bishiyo ya jefa shi ya bar gurin da saurin gaske.........! Sadam! harbi kawai yake saki! ta ko ina! cikin ikon Allah yayi nasarar samunsa a kafarsa...aikuwa a take ya zube a gurin.....! yana rike kafa Sadam! ya 'karasa inda yake cicci'barsa yayi ya sa'ba a kafad'a ya dawo baya sai da yazo yaga babu hanya ko ina a rufe......Ya cika da mamaki a jiye mutumin yayi ya fara kokarin ture silaf d'in domin ya samu hanyar fita inda anan mutumin ya samu nasarar zare bindigar dake jikin wandonsa ya saita kafad'arsa ya sakar masa bulet!!!!!! Ya juyo a fusace! ya dauke shi da mari! faduwa yayi cikin kwatar ya sanya takalminsa ya take masa wuya yana cije baki!! hannu daya ya ture silaf din kana ya sunkuya ya d'auko shi jikinsa jage-jage! da jini ya fito.......Gurin tsit!!! Can Captain Habu ya hangoshi ya fad'i ga jini a jikinsa a guje ya 'karaso gurin yana kiransa idanunsa yaga suna lumshewa jiri ne kawai yake d'ibanshi hannunsa ya rike yana goge masa zufa.....Da bayan bayan daya sojojin suka dawo nan sukaga halin da Sadam din ke ciki gashi dai an samu nasarar kama mutumin amma kuma wanda suke alfahari dashi yana cikin matsanancin hali. 11/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga duk mai bukatar karantawa sai ya tura kudinsa ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank idan kuma katin waya mutun zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din zan fad'a masa yanda zai biya kud'in....08089965176 _07084653262.....Mutanan Nijar idan kuna bukatar littafin to sai ku tura dala dari ta wannan numbars.....90899076 _88137740 katin airtal ko orange.....Dala dari itace a madadin dari uku na najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ _*Na kusa gama free pegea duk me bukata sai ya turo kudin karatu*_ *Free Pege18* Da sauri Captain Habu ya bar gurin, Captain Saleh yazo yazo ya tsaya kawai a kansa yana masa wani irin kallo yaso ace ha'kansa ya cimma ruwa yaso ace bukatarsa ta biya a kansa amma babu komai watarana ya tabbatar da cewar bukatarsa sai ta biya a kansa ya dauki alwashin sai ya salwantar da ransa mutukar suna aiki a guri guda. Mota Captain Habu ya shigo da ita da sauri Captain Saleh ya sunkuya domin taimaka masa sai ya d'aga masa hannu goshinsa duk ya tsatstsafo da gumi hannunsa a kafadarsa ya rike gurin harbin jini kam duk ya jika masa jiki.....Captain Saleh ya matsa gefe guda yana kallo Captain Habu ya rirrikeshi ya kaishi mota, sannan suka tasa 'keyar d'an boko haram! din wanda suka rufe masa fuska da wani ba'kin abu suka daure duk hannayensa da ankwa....Gurin cika yayi da mutane 'yan jarida har sun hallara a gurin mutane sai dauka suke a wayoyinsu da kyar motar ta fita daga gurin.....Cikin brecck din akwai asibiti dake kula da sojoji da iyalinsu kai tsaye can aka nufa da Sadam! wanda tsabar dauriya tasa idanunsa ya kada yayi jawur jijiyar kansa duk ta tashi kana kallonsa a lokacin zaka fahimci yana jin jiki sosai....Lokaci guda likitoci suka rufu a kansa har sai da suka samu nasarar cire bulet! din sukayi aikin gurin yanda ya kamata kana sukayi masa allurar bacci domin ya samu hutu. Rundinar sojoji ta Najeria tayi mutukar jin dadi da faruwar wannan al'amari tabbas sun dad'e suna so su kama koda d'aya ne daga cikin wad'anan mutane domin su kafa hojjoji kana kuma su tsaurara bunkice akansa domin ya sanar musu inda sauran 'yan uwansa suke.....Saboda haka hatta da mataimakin shugaban 'kasa sai da yazo ya duba Sadam! kuma ya jinjina masa a bisa namjin kokarin da yayi....Sannan ya sanar dashi sakon mai girma President yace."Yana gaishe shi da kyau kuma yana jinjina masa hakika ya cika gwarzon maza.......Wannan al'amari yayi masifar 'batawa 'yan adawa rai mussaman Captain Saleh wanda shine mutumin da ya rufe kwatar da silaf din duk dan kar ya samu hanyar fitowa, Sadam! na da ma'kiya a gurin aiki sosai da sosai don wasu ma basu zo duba shi ba sai kananun maganganu ne ke tashi.......A can 'bangaran gida kuma tun misalin karfe takwas na dare suke kiran wayar shi sai dai Captain Habu ya dauka yace."Baya kusa Hjy Fatsima data gaji sai tace Ya fada mata gaskiya idan wani abun ne ya faru Captain Habu ya boye mata....Tun sannan suka sha jinjin jikinsu Sayyada kuka ta hau yi! Hajiya Fatsima ke rarrashinta da ta kwantar da hankalinta babu abinda ya faru.....Alhaji Auwal na kasuwa labai ya riske shi cewar sojoji sunyi nasarar kama dan boko haram! cikin kasuwar bacci amma kuma daya daga cikinsu ya jikkata domin dan boko haram din yayi nasarar harbinsa a kafada.....Ba tsaya wasa ba ya nemi numbar d'an sa to shima dai captain habu ne ya dauka nan yake tambayarshi ya ake ciki Captain Habu yace babu wata matsala insha Allah ya nemi da ya bashi Sadam! din sai ya hau kame kame! kashe wayar kawai yayi ya nufi gida....Yana isa ya tarar dasu cikin tashin hankali da damuwa domin suna zaune suna kallon labarai tashar Bbc news suka nuna Sadam! din akwance kirjinsa daure da bandeji yana jawabi da yanda abun ya faru.........Duk suka tashi hankalinsu Sayyada sai kuka takeyi sai an kaita gurinsa, Sulaiman ne ke rarrashinsa idan ka ganshi sai ka dauka ya damu da al'amarin amma a cikin ransa dad'i yake ji sosai yaso Sadam din ya she'ke barzahu sai ya samu damar auran matarshi Sayyada. Hajiya Fatsima ta sako hijab suka nufi barikin sojojin domin duba halin da d'ansu yake ciki.....Ganinsa zaune yana shan yoght sai hankalinsa ya kwanta Captain Habu ya gaisa dasu Hajiya Fatsima tace"Ka kyauta wato shine ka'ki yi min bayani abinda ya faru sai a tv na gani." Yace."Mamah ai abun alkairi ake fad'a shiyasa ban sanar daku komai nasan da na fada miki a lokacin zakice zaku zo to ganinsa a wannan lokacin zai d'aga muku hankali shiyasa muka bari sai da aka gama komai tukkuna." Alhaji Auwal yace."Alhamdullahi ai da sauki ma al'amarin Allah ya kare ku ya kare ya kuma baku nasara a duk inda zaku shiga." Captain Habu ya amsa da ameen kana ya fita ya barsu domin su gana. Sayyada gefansa ta zauna tana ta kallon kirjinsa inda aka harbe shi tsigar jikinta sai tashi takeyi hawaye kuwa wannan na bin wannan...Sulaiman ya gyada kai ba tare da yace wa dan uwan nasa komai ba ya fice daga dakin ya tsani yaga Sayyada na kusantar inda Sadam! yake. Motarsa ya shiga ya bar barikin sojojin.....A nutse ya gaisa da iyayen nasa yana musu 'karin bayanin kan yanda al'amarin ya faru...Hajiya Fatsima sai da tayi kuka tace"Ni kuwa Da zaka bi shawara ta to da ka ajiye aikin nan Sadam! akwai had'ari a cikinsa." A take ya 'bata fuska yace."Mammah bana son kina irin wannan magana wallahi! tunda na fara wannan aiki bana fata in aje kuma wallahi wallahi wallahi bana yi domin kudi ko wata daukaka ko mukami inayi ne kawai saboda 'kasata Nejaria sannan inayi ne domin taimakon al'umma addua kawai nake bukata a gurunku." Tace"Shikkenan Sadam! Ubangiji Allah ya shige maka gaba Allah ya kare ku a duk inda kuke ya tsare gabanku da bayanku." Suka amsa da "ameen." dukaninsu.......To koda suka tashi tafiya Sayyada ta'ki binsu akayi akayi ta'ki sai ma ta haye kan gadon ta 'buya a bayansa .Alhji Awal yace."A kyaleta ta zauna Sadam! bai so haka saboda abokanan aikinsa na shigowa duba shi to dan ba yanda zaiyi yasa ya hakura suka tafi suka barta. To a cikin mota iyayen maganar suke inda Hajiya Fatsima take cewa''Ni kuwa rashin jituwar Sadam da Sulaiman na bani tsoro Alhaji yara kamar ba 'yan uwa ba ka duba ka gani Sulaiman ne ya dace ya zauna yayi jinyar dan uwansa amma ka lura ko minti biyar baiyi ba ya fita kuma bai ce masa sannu ba wannan al'amari ya 'bata min rai kuma babu babban mai laifi sai Sulaiman din tunda dai shine babba." Alhaji Auwal yana draving yace."Kin san Sulaiman akwai sabga mybe kiransa akayi a waya shiyasa kika ga ya fita bai zauna ba amma na tabbatar zai koma ya duba shi bana so ki sanya wani abu a cikin ranki." Tace."Wallahi al'amarin ke bani mamaki shiyasa nake magana Allah ya dai-dai ta tsakaninsu." Ya amsa da ''ameeen ya rabbi."! *** Kallonta yake itama tana kallonsa idanunta yayi fululu saboda kuka babu yabo babu fallasa yace."Ya kamata ki daina wannan kukan ya isa haka." Ta goge hawayen fuska mirya a dashe tace."Tausayinka nakeji don girman Allah ka daina wannan aikin kaji." Shan kunu yayi yace."Ke! bana son shirme! Wannan aikin idan kinga na bari to bana nuffashi." Hawaye ya sake kwaryo mata, tausayi ta bashi ya sanya hannu yana goge mata hawayen fuska a daure yace."Idan baki daina min wannan kukan ba yanzu zansa Captain Habu ya mai dake gida." Zum'bura baki tayi....Yace."Ni dai na fad'a miki." fuskarta ta hau gogewa da hannunta tana kallonsa shima yana kallonta zuwa yanzu ya gama fahimtar yana da babban matsayi a zuciyar yarinyar yana ganin tsananin sonsa da kaunarsa a cikin kwayar idonta.....Suna cikin wannan hali Captain habu ya shigo da take away a hannunsa, Sai yasa dariya yana fad'in"Kaga laila majnun ko."!! Sadam yayi saurin dauke kansa yana dan harararsa, Yana dariya ya zauna a wata kujera yace"Sayyada lallai kina son abokina da yawa nifa yau na dauka hawayenki ne zai kare." murmushi tayi ta sunkuyar da kanta kasa. Yace."Ga abinci na kawo miki kici." Girgiza kai tayi alamun bata ci. Yace."Me yasa."? A hankali tace"Bana jin yunwa." Kai tsaye yace."Ban yarda ba dole kici wani abu idan kuma kin fiso angon naki ya baki a baki to." Tayi saurin kallonsa yana kwance idanunsa a rufe ya bude yana harar Captain habu din da jin abinda yace.....Captain habu ya mike yana fad'in"Bari in baku guri tun kafin in sha naushi." Dariya tayi tana kallon mutumin nata....Bayan fitar captain habu da minti biyar likita ya shigo da sauri ya kalle ta domin yaga yanayin da take ciki har yanzu hijab dinta na jikinta.....Ta gaishe da dector din shi kuma ya tambaye ta mai jiki tace da sauki....Ya hau duba jikin Sadam! suna hira sama-sama bayan ya bashi magani ya fita ya juyo yana kallonta da d'aurarriyar fuska yace."Kar wanda ya 'kara shigowa kika gaishe shi ranki sai ya 'baci!." Da mamaki ta kalleshi yace."Kinji abinda nace miki ko."? d'aga kanta tayi....Ya mai da idanunsa ya rufe yana jin wani irin kishi a cikin ransa ai dole ne ma ta bar asibitin nan, Muryarta ya jiyo tana fad'in"Ka tashi kasha maganin to."! banza yayi mata tace"Kaji." ya bude idonsa yana kallonta sai ta sunkuyar da kanta...."Sayyada."! ya ambaci sunanta cikin wata iriyar murya.Ta kalleshi yace."Bana bukatar damuwa yanzu kuci abinci ki kwanta ok." "Nifa bana ci."! Tafada duk ranta a 'bace! yace." Kanki kikayiwa ai." Dakin yayi shiru na tsawon minti goma ta mike ta shiga bandakin dake cikin dakin minti uku ta fito tazo ta ra'ba kusa dashi zata kwanta....."Ke! meye haka tashi ki koma kan kujerar can ki kwanta." Abinda ya fada yasa ta maka masa harara! ya kuma ganta ta gyara kwanciyarta a gefansa....."Wai kina so ki dauje min ciwo na ne? idan takura min Zakiyi zan fita in bar miki da'kin." Kuka tasa tana shashshake takaici ya isheshi ya mike zaune da kyar yana kallonta kudundune a cikin hijab tana kuka yace."Kiyi min shiru malama dukanki ko zaginki nayi da zaki cika min kunne da kuka mtswww!. Rage sautin kukan tayi tana goge hawaye yace."Ki kwanta inda kike tunda kin nace! kar ki matso kusa dani balle ki sanya ni a wani hali." Ita dai bata ce masa komai ba ta kwanta......Cikin karfin hali ya mike yaje ya kulle dakin ya dawo ya kwanta minti goma bacci ya daukeshi.....Ta bude idonta tana kallonsa kauna da sonsa da tausayinsa na 'kara nunkuwa a cikin ranta. Itace ra riga tashi taga gari har ya soma haske tana kallon agogo ya nuna mata lokaci karfe shida da kwata na safe da sauri ta sauka taje ta dauro alwala ta fito motsinta shine ya farkar dashi ya mike zaune alhamdullahi jikin da sauki ya mike ya nufi toilet din Alwala yayi ya fito ya tada sallah, kusa da ita........A hankali ta juya tace."Ina kwana ya jiki"? Ya amsa mata babu yabo babu fallasa, mikewa tayi ta zauna gefan gadon hijab din ta cire ya kalleta da d'aurarriyar fuska "Ki shirya idan anjima za'a mayar dake gida ko kuma idan su Mamah sunzo ki bisu." "Saboda me."?tafad'a tana kallonsa....." Ke! ni nake magana kina tambayata." ! ya fada yana kwalalo mata manyan idanunsa....Ba taji tsoro ba sai ma zumbura baki da tayi...."Ko ba kyaji ne."!? banza tayi masa. Duk tausayin kanta ya cikata Yaya Sadam! baya sonta sai wulakantata yake sai idanunta suka soma kawo ruwa, Idanunsa a tsaye a kanta ya gani da sauri yace."Karki kuskura hawayen nan ya zubo." Ai ya 'bata bakinsa don tuntuni hawayen ya tsinke sai kawai ya saki baki yana kallonta Dr ne ya shigo tayi sauri ta 'boye fuskarta cikin hijab, Ganinsa kan dadduma yasa dr fad'in"Alhamdullahi Yalla'bai da alama ba zaka dade a kwance madam ta iya jinya." Hannu ya bashi suka gaisa dr ya duba jikin nasa kana ya bashi magani yana fad'in''Ni zan dinga baka magani da safe Madam kuma ta kula da kai da rana da dare ." Yace."Kai ma na huttashe ka ai ba yaro bane ni zan sha magani da kaina." Dr na dariya yace."A'a Madam ya fi kamata ta baka zakafi samun sauki da wuri." Murmushi kawai yayi dr yayi masa sallama ya fita. Mi'kewa yayi ya isa gadon ya zauna yana kallon bayanta shiru babu wanda yayi magana ya sanya hannu yaja hijab din ta baya ta rike wuyanta da sauri ta juyo tana kallonsa, Sai ya saki hijab din ya kwanta rigingine ba tare da yace mata komai ba ita kuma hakan da yayi sai ya sake tunzura ta ta mike zata fita daga d'akin!....."Sayyada."!!! Ta jiyo muryarsa na kiranta ko kallonsa ba tayi ba ta bude kofa ta fita, sai suka ci karo da Captain Habu da Saleh zasu shigo dake kofar a bude take duk yana hangosu yana kallon tana gaishesu har shi Captain Saleh din da yake mata wani irin kallo.....Ransa ya 'baci! yarinyar nan ta raina shi wato yace kar ta fita sai da fita! ga matsiyacin nan yana kallonta Captain Saleh anyi d'an akuya......Habu yace."Sayyada ina zakije." ? inda inda ta hau yi yace."Muje ciki." gaba tayi suka rufa mata baya........Xaune suka same shi fuskar nan a murd'e fatar goshinta duk ta tattare kana kallonsa zaka fahimci ransa a 'bace yake. 12/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga masu bukata zasu tura kudin ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars zan fada mata yanda zata biya kudin....08089965176 _07084653262.......Mutanan Nijar idan kuna bukata to zaku tura dala dari ta wannan numbar....9089976 _88137740 katin airtal ko orange Dala dari uku kudin Najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ _*Na kusa gama Free Peges ga duk me bukata sai ya garzayo ya biya kudin karatu*_ *Free Pege19* Jiki a sanyaye taje bayansa ta zauna tare da rufe jikinta da hijab idanun saleh na kanta sai ya soma zargin wani domin shi duk abinda akeyi bai sani ba bai san cewar Sadam din yayi aure ba tunda ba shiri suke da juna ba, ammafa ganin farko da yayiwa yarinyar ya kwadaitu da ita tabbas idan ta kasance matar Sadam! ce ita to kuwa duk yanda zaiyi sai yayi ya biya bukatarsa ko dan ya kashe sadam din da bakin ciki Sakin fuska yayi tamkar ba mugu ba ya duba sadam din yana tambayarsa jiki duk gurin sai da sukayi mamakin sauyawarsa lokaci guda Sadam kam baiyi wani mamaki savoda yasan Saleh ba karamin makirin mutum bane. Duk da yayi kokarin danne 'bacin ran dake damunsa amma duk da haka Habu ya fahimci yana da damuwa,Sama-sama suka gaisa da abokanan aikinsa inda ya na hankalce da inda Captain Saleh yafi mai da hankali gurin kallo sai yaji tamkar ya tashi ya Nausheshi saboda takaici, Captain Saleh mayen mata ne shi yasa kwata-kwata baya son zamanta a bracck din saboda irin su Saleh a kwai hadarin gaske......Hira sukeyi sama-sama, ba tare da ya sanya musu baki ba, Sai da ya gaji da abinda Saleh keyi masa yace."Ya kamata fa ku shiga ofis naga lokaci ya wuce." Dukaninsu suka mike sukayi masa sallama, Saleh har da waiwayen Sayyada saboda tsabar jaraba. Suna fita ya mi'ke zaune yace."Ke! juyo nan ki kalleni." Juyowa tayi tana kallonsa kana kallonta kasan a tsorace take domin miryar da yayi mata magana kamar ba ta mutum ba. "Baki isa kizo ki zubar min da mutunci ba." Ya fad'a yana zare mata ido! ya cigaba da cewa meye amfanin xamanki anan da zakice dole sai kin zauna tare dani me kike tsinana min ? daga anyi magana sai ki hau kuka bakyajin maganata nace dake Karki fita sai da kika fita ni da bakina nace kar in kara jin wani namiji ya shigo kin gaisa dashi saboda ban isa ba naji da kunnena kina gaisawa da Saleh! To yau d'in nan zaki bar brecck din nan ko 'kinki ko kinso idan kukan jini zakiyi sai dai kiyi na gama magana."""" Shiru tayi masa idanunta ya kad'a yayi jawur! Sadam baya sonta yanzu meye laifin wanda ya kula da kai da rayuwarka kan kawai tace zata zauna tare dashi yake wulakanta, Hawayen da take ta kokarin dannewa suka fara zuba.....Yana jinta tana shashshekar kuka yaki kallonta lumshe idonsa ma yayi bacci na daukarsa,Motsin bude kofa yaji ya bude ido ita kuma tayi saurin sanya gefan hijab dinta ta kare fuskarsa. Sulaiman ne ya shigo cikin Shadda galila 'yar gasken anyi masa d'in 'yan birni yayi kyau sosai kamshi ne kawai yake tashi a jikinsa. Babu yabo babu fallasa ya amsa sallamarsa Sayyada najin muryar Sulaiman ta bude fuskarta, Sulaiman ya karaso bakin gadon ya tsaya yana kallon Sadam! din A hankali yace."Ya jiki."? "Alhamdullihi." Yafada ba tare da ya kalleshi ba. "Yaya Sulaiman ina kwana ya kwanan Aunty Luba."!? Ya Juyo yana mata wani sihirtaccen kallo fuska a sake yace." Lafiya lau baby Sayyada dake haka yake kiranta tun tana yarinya ya cigaba da cewa "Ya mai jiki? ina fatan komai lafiya." Da gefan ido ta kalleshi taga ya wani ci kunu! gabanta na faduwa tace"Jiki da sauki wallahi." Shiru dakin yayi Sadam! na mamaki wato duk hargagi da masifar da zaiyiwa yarinyar ba zata ji maganarsa ba dole ya koya mata zama. Sulaiman ya kalleshi a nutse yace."Babu abunda kake bukata ko? Ko da yake ma naga jikin da sauki Allah ya takaita wahala." Wannan magana da Sulaiman din yayi ta tun zura masa zuciya domin shi a yanda ya fassara maganar kamar ta rainin hankali ne *Allah ya takaita wahala* Idan bai manta ba akwanakin baya Sulaiman ya sha cewa dashi ya rabu da aikin soja saboda a cikinsa akwai babban kalubale sannan mutum yazo ya mutu a banza a wofi bai cimma shekarunsa....Wannan magana da ya fad'a ta nuni da irin maganganunsa na baya....Kamar ya bashi amsa dai-dai dashi sai kawai ya kyaleshi domin baya so su raba hali a cikin mutune amma hakika abinda Sulaiman din keyi masa ya soma wuce makadi da rawa. Hira sukeyi yana jinsu dama can yasan akwai shakuwa a tsakaninsu bai wani damuba tunda bai ga an wuce gona da iri ba, shine dalilin da ya sanya ya rabu dasu suke maganganunsu na can Garinsu *Dabi* Bai tanka musu ba ya dai kasa kunne yana jinsu........"Sadam! ni zan wuce kasuwa Allah ya sawake, ya ta'kaita wahala."! Sai ya bud'e idonsa da saurin gaske ya mike zaune " Dakata malam kar ka fita tukkuna sai ka tsaya ka fad'amin ma'anar wannan kalmar da kake ta nanatawa tund'azu."!! Cikin 'karfin murya yake maganar yana wani irin haci!!! Sayyada cikinta duk ya d'ori ruwa mutum ma na kwance bai da lafiya amma ba zai bar masifa ba. Murmushi yayi yace."Saboda nayi maka addua kake tuhuma Sadam! *Allah Ya takaita wahala* yanzu ma na 'kara fad'a." Ya fad'i maganar yana d'aga kafad'a alamun bai damu ba. Yace."Kai! baka isa kayi min addua ta kar'bu ba ka sani Allah na kar'bar adduar mai kyakkyawar niyya ne me kyawun zuciya kai kuwa fa kullum zuciyarka ba'kikkirin take baka nufin mutun da alkairi sai sharri Ni! nafi karfinka wallahi baka isa kayi min abinda Allah baiyi min ba, bana nadamar na rasa raina a aikin soja! saboda nasan nayi aiki domin Allah da mazonsa zan samu kyakkyawan sakamako gurin Allah." "Ni kake fad'awa wannan maganar."! ? Sulaiman ya fad'a ransa a mugun bace."! " Kai wanene!? da ba za'a fad'a maka magana ba."! shima ya mayar masa a zafafe."!!! "Yaya Sulaiman kayi hakuri don Allah." Murya na rawa take maganar."! "Kika 'kara wata magana anan gurin sai ranki ya 'baci!! wallahi."! Yafad'a yana watsa mata mugun kallo...Mi'kewa tayi tana kuka " Wannan wane irin hali ne? yanzu meye laifin Yaya Sulaiman kuma? kawai don yayi maka addua aikin soja ai ba hauka bane." Bai san sanda ya dirgo daga gadon ba ya nufeta....Sulaiman na ganin abinda yake shirin yi yaje ya tare shi!!! "Karka kuskura ka daketa wannan ai hauka ne! dama dukaninku haka kuke ku kama matanku kuna jibga sai kace bayi."! Wani wawan! naushi ya kir'ba! masa a 'kirji! Sulaiman ya ri'ke kirjinsa yana tari! azabah! na sukanshi.....Gefe ya tureshi yaja tsaki tare da fad'i " Haka sai kace namiji ashe rago ne."!!! Sulaimai ya sake yunkurin kare Sayyada...."Wallahi karka kusantoni sai nayi maka illah! ka bar ganin kirjina daure da bandaji bani da dad'i!!!! Sulaiman ya tsorota da Sadam! domin ga dukkanin alamu allurar ce ta motsa kai Soja bala'i ne.....Sayyada ta makure jikinta a bango Rumfa yayi mata ya sanya hannu ya sha'keta mata wuya"!! Don Ubanki maimaita abunda kikace yanzu, wato kema kin fara daukar hud'ubarsa ko? kina nema ki zagemu ki zagi aikinmu? hakane ko ba haka bane."!? Cikin hargagi yake maganr....Hawaye sai tsere suke a fuskarta "Kayi hakuri don Allah ba zaginka nayi ba."!? " Ni da Sulaiman waye mijinki kuma maganar wa yafi cancanta ki dauka."? da karfin murya yake maganar....Tace"Kaine mijina kuma maganarka yafi dacewa na dauka." "Ok me yasa idan nace karkiyi abu sai kinyi raini ne ko me."!? Girgiza kai tayi..." Kayi hakuri kayi hakuri kayi hakuri."! abinda take fad'a kenan....Wuyanta ya saki ya koma ya kwanta yana wani irin nishi! kirjinsa ya rike! da alama ya fama gurin harbin.... Sulaiman na tsaye yana kallonsa yana nishi!! jini daga jikin bandejin yana fitowa saman kirjinsa, bai wani damu ba ya kad'e rigar jikinsa ya fice daga d'akin zuciyarsa tas yaji dadin yanda ya tashi ciwon nasa shine wahalalle wanda wahala ta yankewa cibiya Allah yasa ma gurin ya lalace ya jima a kwance yana jinya. Ganin yanda yake rirri'ke kirjinsa da kuma jinin dake zirarowa yasa hankalinta yayi masifar tashi da sauri ta bude kofa ta fita Minti biyar suka shigo da likita hankali a tashe ya isa inda yake ya soma duba gurin mikin yana tambayar Sayyada garin ya akayi haka ta faru ita dai ta kasa cewa komai sai kuka takeyi Sai da taga jinin dake zuba ya tsaya sannan hankalinta ya kwanta amma dai duk da haka hawaye bai daina zuba daga idonta ba.....Dr ya kalli Sadam! dake rintse ido yana cije lips yace.."Wai Yallabai ya akayi haka ta faru ne."! Ido a rufe yace."Bacci nakeyi na danne gurin." Dr yace."Ayya Madam kina gani a maimakon ki zauna kusa dashi shine amfanin zamanki a gurin ai idan da matsala ko zamu kawo maka mai kula da kai ne."? girgiza kai yayi alamun baya bukata. Sayyada tace"Tsautsayi ne Dr nima bacci nakeyi shiyasa ban lura ba." Yace."Ai naga alama a yanda kike son Yallabai ba zaki bari hakan ta faru ba sai da dalili." Murmushi tayi mai ciwo tana tuno rashin mutuncin da yayi mata d'azu. Dr Yace."Idan yayi break ki bashi magani kinji ko." Tace."Insha Allah." Bayan fitar Dr din dakin yayi shiru sai saukar numfashinsu ido ya bude yana kallon inda take tana can takure kan kujera taki kallonsa haushinsa takeji sosai tana da zuciya dole tayi taka tsantsan da rashin mutuncinsa. Ya jima yana kallonta tausayinta yake ji yanzu kuma nadamar abinda yayi mata yake....Tsaki yayi cikin ransa koma meye ya.faru itace ta jawowa kanta. Hajiya Fatsima da Alhaji Auwal ne sukayi sallama. Sayyada ta amsa da sakakkiyar fuska tana gaishesu....Hjy Fatsima tayi ta naxarinta taga tabbas akwai damuwa a tare da ita ga idanunta sunyi jawur dasu.....Sadam! ya gaishe da iyayen nasa cikin dauriya da kokarin danne abubuwan dake damunsa Nan Alhaji Auwal yake tambayarsa ko Sulaiman yazo yace."Bai jima da fita ba....Ya tambaye shi yanayin jikin nasa yace."Da sauki bashi da wata matsala...Godiya yayi ga Allah yayi musu sallama kasuwa ya wuce kai tsaye. Hajiya Fatsima tace"Sayyada ga abun kari nan na kawo muku ki karya sai ki had'awa mijin naki shima." Tace."To Mammah! tea ta had'a me kauri ta zuba soyayyan dankali da kwali ta dauka gadon da yake kwance ta nufa ta zauna gefansa a hankali tace"Ka tashi kayi break kasa magani." Sai da tayi magana sau biyu sannan ya mike zaune da dubara ya kar'bi kofin tea din....Ta mika masa tare da dora masa plate din dankalin a cinyarsa....Da kyar yake daga hannunsa yana kur'bar tea din saboda kafad'arsa ta dama harbin yake, kamar ta kar'ba ta bashi da kanta sai tayi wa kanta fad'a tasan hali zai iya gwaleta ko ya hantareta. mikewa ma tayi ta bar gurin tea ta hada ta zauna kusa da Mamah tana kur'ba amma hankalinta na kansa da kyar ya shanye tea din dankwalin kuwa bai fi uku yaci ba yace."Zo ki dauke plate din nan." Ta mike da sauri ta isa ta dauke masa....Ruwa ta dauko ta dawo gurin ta 'balli maganin ta mi'ka masa kar'ba yayi ya watsa a bakinsa ya kora da ruwa, Hjy Fatsima tana kallonsu cike da farin ciki a gaskiya ta yaba kwarai da yanda Sayyada take kula da Sadam!!! Bai kai rabin awa da shan maganin ba bacci ya daukeshi....Nan Sayyada da Hjy Suka dinga hira Sayyada ta saki jikinta sosai da ita tana daukarta tamkar mahaifiyarta. Sai kusan karfe daya sannan tayi niyar tafiya tace zasu dawo da daddare sannan tana komawa gida zata sanya baban gida ya kawo musu abincin rana." Sayyada kamar ta bita saboda abinda yace mata dazu *Banga abinda kike tsinana min ba saboda haka idan su Mamah sunzo dole ki bisu ku tafi gida* Wannan magana ta bata haushi mutuka amma duk sanda ya sakeyi mata irinta to sai dai ya nemeta ya rasa. Sallah tayi ta koma gefansa ta zauna mifici ta dauka tana masa firfita duk kuwa da cewar akwai fanka a dakin idanunta kurrr gurin ciwon tana mamakin jinin da ya dinga tsiyaya d'azu. Idanunta taji suna lumshewa alamun bacci na soma ya dauketa dama tasan za'a rina mutukar ta ci bashin bacci to duk inda ya kamata sai tayi take jin dadi.....A hankali ta ra'ba gefansa ta kwanta tana kallon fuskarsa, 'Kare masa kallo take sosai tana gazgata maganar mutane inda suke cewa duk family nasu ya fisu kyau sai dai su nuna masa hasken fata, ita yanzu kalar fatarshi ma burgeta take, ta tsurawa karamin bakinsa ido wanda wani bakin gashi me gazarzar! ya kewaye lebunansa lumshe ido tayi gabanta yana faduwa....Ta sanya hannu a hankali ta shafo kirjinsa! tare dashi suka sauke ajiyar zuciya, cike da tsoro ta zare hannunta gabanta na dukan uku uku!!! Sadam! bai san wainar da take toyawa ba kawai ajiyar zuciyar ce tazo a lokacin......minti biyu ta sake d'ora hannunta kan kirjinsa, Ta lumshe idonta tsigar jikinta sai tashi takeyi......Haka bacci mai nauyi ya dauketa. Idonsa ya bude a hankali sai ya ganta kwance a gefansa hannunta a kirjinsa ya jima yana kallon hannunta ya kasa daukewa....Gyaran murya yayi tayi saurin bude idonta a firgice ta mike zaune! kauda kansa yayi ya mi'ke zaune itama mikewa tayi ta nufi toilet ta wanke baki ta fito....Tana kallonsa yana kokarin sakkowa daga bed din tana jin tsoron tunkararsa bata son hayaniya da hargagi ta lura shi kuma komai lalura baya fasa halinsa. Yazo ya wuce ta ya shiga bandakin alwala ya daura bayan ya wanke bakinsa ya fito fuska a daure Sallah ya tayar yana idarwa akayi knocking din kofar...kallonsa tayi ya watsa mata harara! tayi kasa da kanta.....Mikewa yayi yaje ya bude kofar....Baban gida ne da kwandon abinci anan ya dakatar dashi ya karbi kwandon abincin Baban gida ya dubashi yana masa sannu da jiki ya amsa babu wata cikakkiyar walwala kisin Sayyada ne kawai ke sasakar ransa ta riga ta gama nuna masa matsayinsa ta nuna masa tafi kaunar Sulaiman a kansa ba tun yau ba dama ya fahimci akwai wata a 'kasa a tsakaninsu." Ajiye kwandon abincin yayi bai ce mata komai ba ya haye gadon wayarsa ya dauka yana dubawa.....Ganin lokacin shan maganinsa na nema ya wuce tace"Ko na had'a maka abincin kaci kasha magani." Idab dotse na magana to shima zaiyi ya shareta yana duba waya......Ta'be baki tayi duk yana kallonta ta 'kasan idonsa ya girgiza kai fuskarsa a daure Yace."Ke!!! ba cewa nayi idan Mammah tazo ki bita ba ke wace irin mara zuciya ce ne."!? taji wani sagewar jiki!! da jin abinda ya fad'a ido ta zuba masa tana kallo Cikin shan mur! yace."Da daddare ba sai na sake yi miki magana tana zuwa sahunki a likkafa ki bi bayanta."! Shiru tayi masa bakin ciki na sasakar zuciyarta......Sunanan zaune akayi Nocking din kofar a karo na biyu." Tashi kije ki bud'e."Ya fad'a hankalinsa kan waya, kamar kar ta tashi sai ta mike taje ta bud'e kofar suka had'a ido da ita tana sanye da ingilish wear riga da seket tayi rolling da karamin mayafi fuskar nan taci mai tayi make up kamar hauka ido ta sanya masa gashi sai kace aljannu hannu rike da key na mota da karamar pose Halima 'Yar gidan General AbdulSalam Shugaban sojojin Najera kenan....Wani matsiyacin kallo ta watsa Sayyada ta tsartar mata da yawu" Bani hanya na wuce."!! tafad'i cikin izgili da d'agawa! Sayyada bata san sanda ta kauce daga hanya ba tana kallo ta shige ta barta a tsaye a gurin. Jingina jikinta tayi a bango tana kallon ikon Allah.....Halima ce ta isa inda yake ta d'ora kanta a gefan kirjinsa tana shashshekar kuka!" Sweetheart abinda ya same ka kenan! wayyo na shiga uku ina can Gombe gurun bikin kawata Captain Saleh ya sanar dani halin da ake ciki me yasa kai baka fad'a min ba." A marairace take maganar." Har yanzu kanta na damtsen hannunsa na hagu......Motsi yayi yana so ya tashi fuskarsa da akwai alamun sassauci yace."Halima abun alkairi shi ake shela ba irin wannan ba dama kin tsaya a inda kike kin gama shagalin bukinki." "A gaskiya Sweetheart baka sona ta yaya zan iya xama a wani gurin kana cikin wannan hali karfa ka manta da cewar kaine za'bin raina farin cikin zuciyata." Sayyada taji wani irin gumi mai d'umi!! na tsiyaya a jikinta....Ido jawur take kallonsu shi kuma sai murmushi yake kamar bashi ne masifaffan nan ba.....Inda suke ta nufa ta tsaya kansa"Baiwar Allah daga ina? kin shigowa mutane daki babu sallama babu neman iso sai kace wata kafura ai kafuran ma suna sallama da Hi ko makamancin hak" Wani wawan kallo Halima kewa Sayyada cikin nuna ke wacece tace"Ke! ni kike fad'awa wannan maganar."? Sayyada tace"Baiwar Allah ba magana bace gyara ne nayi miki domin naga alamar kina yin abu irin na marasa hankali." "Kutttt!!!! Sweetheart wannan wace jahilar yarinya ce take min maganar banza yanzu zan sanya a daureta wallahi." Ya kalli Sayyada yana wani cin mur!!! "Ke bar gurun nan kinzo kin tsaya kan mutane saboda rashin tarbiya." "Wallahi ba zan bar gurin nan ba.." Tafad'a cikin fad'awar gaba ga dukanin alamu matar nan nada matsayi mai karfi a gurinsa......"Wai Sweetheart wannan yarinyar a ina ka samo ta dagani 'yar kauye ce duba da yanda take maganar *He da He* ." Dariya ce ta kusa kufce masa yanda Halima ta fad'i maganar sharri ne kawai amma Sayyada bata irin wannan maganar ta *He da he* "Zaki bar gurin nan ko sai na sanya yanzu anzo anyi waje dake." Halima ce tayi wannan magana cikin hayaniya....Sayyada ta gyara tsayuwarta har da rike karfen gado tace"Sai dai in kece zaki fita daga dakin nan wallahi baki isa ki tambaye shi matsayina a gurinsa."! Halima ta kalleshi wanda ya zuba musu ido kawai yana kallo Tace"Sweetheart bana son munafurci shin kai ma ka soma tara mata irin nasu Saleh." Yace."Ke bana son hauka malama wannan kanwata ce ita." Sayyada tace"Meye zaka 'boye mata kace mata ni matarka ce in yaso kome zatayi sai tayi." Halima ta mike tsaye a zabure! tana fad'in"Da gaske take wannan maganar data fad'a."!!!! 'Karamin tsaki yaja "Ke! kinga nayi kama da wanda zai auri wannan 'yar 'kauyen Halima."! Tace." Nima dai haka na gani Sweetheart. " Sai ta koma ta zauna tana yiwa Sayyada kallon banza....Sayyada takaici ya turnuketa lallai Yaya Sadam! ita yake dizgawa gaban mutane......A zuciye tace"Ke Karuwa tashi ki fita daga d'akin nan ko kuma in tara miki jama'a."!! Halima tace"Ke!!! ni kike kira da karuwa don kutumar ubanki kin san waye ubana kuwa."!?? Sayyada tace"Oho! miki ko waye ubanki bai dame ni ba." A zafafe! Halima ta tsinka mata mari! ta sha'ke mata wuya ga hijab a jikinta......."Ke!!! Halima saketa."! yafada cikin karfin murya."Sweetheart kana jin abinda take cewa ko."!? "Eh naji saketa." Halima ta saketa tana huci!! Sayyada ta karkad'e hijab dinta ko a jikinta itama sai huci take....."Sayyada fita daga d'akin nan."!! cikin tsawa! yayi maganar da nufin tozarta mutum. gwiwowinta duk sukayi sanyi ta kalleshi ya ware mata manya manya idonsa wanda sai zaiyi rashin mutunci yake bud'esu."Ko bakiji abinda nace ba Fita a d'akin nan."!!! Wani 'karfin zuciya yazo mata tace"Ko baka fad'a zan fita yanzu." 'Kofar fita ta nufa zuciyarta na wata iriyar tafarfarsa..........! 13/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga masu bukata zasu tura kudin ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars zan fada mata yanda zata biya kudin....08089965176 _07084653262.......Mutanan Nijar idan kuna bukata to zaku tura dala dari ta wannan numbar....9089976 _88137740 katin airtal ko orange Dala dari uku kudin Najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ *Wannan shine Last Free Pege* *Free Pege 20* Da sauri ta bude kofa ta fice daga dakin zuciyarta na wata irinyar tafarfasa rarraba ido take a harabar gurin....Kai tsaye kawai sai ta nufi 'katon gate d'in da yake cike da sojoji ko tsoro ba taji burinta kawai ta fice daga bracck d'in bata ta'ba tsammanin Sadam! zaiyi mata irin wannan wulakancin ba, tana tafiya tana share hawayen bakin ciki tayi tayi ta tsayar da hawayen abun ya fassakara dole ta kyalesu suna zuba Bayan fitar ta daga d'akin saboda ya san wautarta sai ya dauki wayarsa ya kira d'aya daga cikin sojojin dake bakin gate din yace."Za suga wata yarinya ta fito 'yar kimanin shekaru 15 ko kasa da haka tana sanye da atamfa blue kar su barta ta fita......Aikuwa hakane ya faru Sayyada na isa suka tare mata hanya tayi tayi su bude mata suka 'ki kawai sai ta nemi gurin bakin gate din ta sanya kukan bakin ciki. Lokacin da yake wayar Halima ta sha'ka da yawa bayan ya gama wayar tace"Wai menene idan ta fita da zaka damu nifa jikina ya soma bani akwai wani abu a tsakanika da yarinyar nan wallahi." Yace."Babu wani abu a tsakaninmu na fad'a miki kanwata ce karki damu." Dake ta saba da wannan dad'in bakin nasa sai ta warware tace"Ya maganar auranmu to." ? kallon shashasha! yayi mata yace."Ashe baki aje wannan maganar a gefe ba kenanan."! Halima ta tunzura tana huci! tace"Wallahi ba zan ajiye maganar nan ba har sai na cimma burina akanka kome zakayi min zan jure.''Shiru yayi mata kawai.....Ta cigaba da cewa"Yanzu ka bakaji kunyar fada min wannan maganar ba? wane irin sone ban nuna maka ba zakace na ajiye maganar aura a tsakanina da kai insha Allahu kamar anyi an gama." Kallon mahaukaciya kawai yake mata yo shi wannan ko da matan duniya zasu kare baya ta'ba jin xai iya auranta......Wayarshi ce tayi kara yana dubawa yaga Mu'azu daya daga cikin sojojin bakin gate yace."Yallabai yarinyar nan fa gata ta zauna tana turjiya kan hanya kuka kawai takeyi." Yaji wani iri a jikinsa jin abinda Mu'azu yace."Please Mu'azu kayi kokarin kawo min ita dakin dana ke kwance." Mu'azu yace."Okey insha Allah." Babu irin rarrashin da Mu'azu baiyi mata ba amma fafur ta'ki binsa ita dole sai sun bude mata kofa ta fita.....Mu'azu ya kara kiran numbarsa a karo na biyu Yace."Kayi kokari ka bata wayar kace zamuyi magana." Nan ma Sayyada ta'ki kar'bar wayar zuwa yanzu ta daina kukan sai dai bakin ciki dake cin zuciyarta.....Koda Mu'azu ya sanar dashi cewar ta'ki kar'bar wayar sai hankalinsa ya tashi har ya yunkura zai tashi da nufi yaje ya dawo da ita sai zuciyarsa ta raya masa cewar kar yaje ya rarrasheta mutuncinsa zai zube a gurinta....Ya koma ya kwanta fuska a cud'e!......Halima kam tana ganin hankalinsa ya tashi kan yarinyar sai ta fashe da kuka ta mike a zafafe take farfad'a masa ba'kaken maganganu....Wanda suka sanya ya buga mata muguwar tsawar da ta sanya ta d'ibi takalmanta a hannu ta fice daga dakin......Hankali a tashe ta nufi bakin gate d'in ganin Sayyada a tsugune ya sanya ta isa inda take ba tare da tace mata komai ba ta mikar da ita tana girgiza kafadarta ''Ki fad'a min gaskiya meye alakarki da Sadam! Dazu kinyi wata magana wacce ta sanya jikina yayi sanyi don girman Allah karkiji tsorona." Sayyada tace"A kan me zanji tsoronki Ci kike bani ko sha ko kuma aljanna kike rabawa da zanji tsoranki gaskiyar magana shine Ni Sayyada matar Sadam! ce yau kwananmu shida da daurin aure." Halima ta silale a gurin ta fad'i ji take kamar ta d'ora hannu aka tayi ta kurma ihu!!! gumi duk ya jikata....."Ni Sadam! zai yaudara jama'a!?? Hawaye ne suka soma kwarya a fuskarta Sayyada ta saki baki tana kallonta wai kuka take kan d'a namiji lallai bata da hankali....To ganin Halima na hawaye sai hankalin sojojin nan ya tashi sanin wacece halima yasa suka fara gutsi tsoma a tsakaninsu suma sai yanzu suka fahimci cewar ashe Sayyada itace amaryar Sadam! da yaje can kauye aka aura masa lallai Sadam bai kyauta ba kuma a zahirin gaskiya ya yaudari Halima domin ta sakankance da cewar zai aureta amma ya yaudareta. Mikewa tayi a jigace ta gyara yafan mayafinta ta dauko pose dinta ta koma dakin da Sadam din yake......Ya mike tsaye idanunsa a kan kofa yana so yaga shigowar yarinyar halima ta fado dakin yanda ya ganta a Jigace sai da gabansa ya fad'i yasan hali bata da hankali yanzu zatayi masa hauka sai ya daure fuska tamau! yana kallonta yace."Ba cewa nayi ki fice ki bar min daki ba tunda kema b......Bai karasa ba ta daga masa hannu "Rufe min baki bakin algungumi azzalimi! Sai ya saki baki yana kallonta tace" Nan ka fada min cewar yarinyar kanwarka har da rantsewa yanzu kuma ina fita ita ta tabbatar min da cewar matarka ce yau kwana shida da daura muku aure Sadam! ni zaka yaudara? ashe dama xaka iya yi min haka a irin kauna da son da nakeyi maka."? tana hawaye take maganar....Tausayi ta bashi yace."Kinga Karki dauka wannan auran zaiyi tasiri sam! bana son yarinyar kawai umarnin iyaye na nabi amma ke kanki kin san yarinyar ba sa'ar aurena bace idan kin kwantar da hankali ki nan gaba kadan zata zama 'yar aikin gidanki." "Ai na daina yarda da wad'anannan kalaman naka na yaudara wallahi ka bani mamaki Sadam! ashe kai mayaudari ne ban sani ba." Shan kunu yayi yace."Idan kin san ba'kaken maganganu zaki fad'a min to sawunki a likkafa ki kama hanya ki fice idan raina ya 'baci ba zakiji dad'i ba." Kallonsa tayi taga yaci kunu tasan halin rashin mutumcinsa idan abun ya motsa masa duk da bashi da lafiya zai iya dukanta.....Tace"Idan ni 'yar halak ce daga yau na rabu da kai." tasa kai ta fice daga d'akin....Kafad'a ya d'aga alamun abun bai dameshi ba ya isa bakin kofar ya tsaya yana kallon dambarwar dake faruwa tsakanin Sayyada dasu Mu'azu.......Ana budewa Halima gate Sayyada tayi waje da gudu Halima ta fice da motarta. Yaga lokacin da ta fita daga bracck din sai ya koma dakin a gaggauce ya kira lamar Habu. Yana dagawa yace."Habu duk abinda kake ka aje yanzu yanzu yarinyar nan ta fita ban san ina ta nufa ba." Captain Habu yace."Wace yarinyar wai."! Cikin kufula yace."Sayyada fa nake nufi."!! Habu ya kashe waya hankali tashi ya fito daga ofis gate aka bude masa ya fita can ya hangota tana tafiya gefab titi ya bi bayanta da sauri Sayyada najin sahun mutum a bayanta ta waiwaya sai taga Habu ne ranta ya 'baci itafa ba xata koma ba ta riga tayi alkawari....To da yake tafiyar ba daya bace Captain Habu ya iske gabanta ya tare yace"Sayyada ina zakije yanzu wa kika sani ? kika fito kan titi kina tafiya."! Ta share hawayen dake zubo mata tace"Zan koma *Dabi* ne." Akan wane dalili Sayyada me yayi xafi."!? Sai ta fashe da kuka ta tsuguna a gurin.....Tausayi ta bashi ya dinga rarrashinta sai da yaga tayi shiru sannan yace."Sadam! ne yayi miki laifi ko."? Daga kai tayi yace."Kiyi hakuri da abokina yana da zafi ne amma kuma mutum ya iya zama dashi mutum ne mai saukin hali ki taso mu koma yanzu haka shine ya turo in daukeki." Tace"YaYa Habu ni bazan koma ba tun jiya yake min masifa motsi kadan fad'a da kyara da hantara me nayi masa kawai don yaga ina sonsa shine fa ya koroni daga dakin saboda budurwarsa. Cike da mamaki! yace.''Budurwarsa kamar yaya." ? tace"Wata Halima ce tazo shine ta zageni shima yace na fita." Captain Habu ya girgiza kai yasan za'a rina wai an saci zanin mahaukaciya Halima tazo kenan to Allah ya rufa asiri....."Kiyi hakuri Sayyada zan nuna masa kuskuransa har yaushe ne xaka fifita budurwa kan matarka ta sinna kiyi hakuri kinji ko ki zama jarumar mace mai juriya kan komai." Captain Habu yana da mutuncinta a idonta shine dalilin da yasa kawai ta hakura ta bishi suka koma cikin barikin sojojin. Yana hango zuwansu ya koma cikin dakin hankalinsa ya kwanta shi kanshi ya rasa gane meke damunsa kan yarinyar yana kishinta mutuka haushin abinda tayi masa kan Sulaiman ne yasa ya koreta......Sai da suka hau sama suka fad'o da Habu sannan suka rabu Captain Habu ya nuna masa abinda yake bai dace ba ko babu aure a tsakaninsa da Sayyada kanwarsa ce bai kamata ya fifita wata akan ta ba, da yaga Habun ya dauki zafi sai ya shareshi ya nemi guri ya kwanta har da lumshe ido....Captain Habu ya kalli Sayyada yace"Idan yayi miki wani abu da bai gamsheki ba to ki sanar dani ai shima yana da na gaba dashi kuma a dokar aikinmu bamu yarda da cuzgunawa matanmu ba." Jin abinda Habu din yake fada mata yasa ya bude ido yana harararsa yace."Zaka zugata ne tayi min rashin kunya dama ba ganin mutuncina takeyi ba."! Habu yace."Ni ba zugata nake ba ina koya mata daburu ne da yanda zata kwaci kanta a hannunka saboda na lura kai din ka fiye son kanka da yawa." Miskilin murmushi yayi ya mayar da ido ya rufe....Captain Habu yace."Me kike so na siyo miki in anjima." Tace."Babu komai."! yace."ki bari zan siyo miki shawarma! kici abinki karki bashi." murmushi tayi tana mamakin karamci da kyautayi irin na Habu. Bayan Captain Habu ya fita sai dakin yayi shuru Sayyada tayi kici kici da fuska taki kallon inda yake kwance tayi alkawarin ai ta daina rawar jiki a kansa ballanta har ya samu damar wulakantata. Bude munafukan idanunsa yayi yana kallonta amma sai ka rantse da Allah cewar ba ita yake kallo ba......Yanzu tausayi take bashi sosai gyaran murya yayi wai ko zata juyo ta kalleshi yaga ko da wasa bata juyo ba ya cika da mamaki kwarai! sai ya fara d'an tari! a hankali a hankali to wannan karon ta d'an juyo amma babu walwala a fuskarta da dane da tuni taje inda yake tana rawar jiki sai yaga motsi ba tayi ba a inda take........dauke ma kanta tayi ta dora kafafunta duka kan kujera ta juya masa baya. "Ke!!!." Ya ambata tasan da ita yake sai ta shareshi "Ko bakya ji ne."!? Sayyada ta ci kunu ta'ki amsawa ballanta ta kalleshi idan ya gaji ya kira sunanta. " Sayyada." Ya ambaci sunanta cikin kasalalliyar murya...Kallonsa tayi tana zum'bura baki! "Kina ji ina magana kinyi banza ko."? " To ai ba sunana "Ke! ba." "Okey naji ina maganina."? " Nima ban san inda yake ba." Tafada tare da dauke kanta........! shiru yayi mata ya koma ya kwanta dama dan dai yayi mata magana ne yasan ba lokacin shan magani bane. Dake dakin da tv sai ta kuna kallo ta rage vollom Wani indian film take kallo hankalinta ya dauke kan film din ana soyayya Sharukan da Saif Ali khan sai preetyzeenta filim din na soyayya ne sosai ya burgeta ita dai a cikin ranta tafi son yarinyar ta auri Sharukan a ganinta sunfi dacewa.....Sadam! na ganin yanda ta mai da hankalinta kan film din cikin zuciyarsa yace."Yarinyar "yar soyayya ce.....Ganin magariba ta gabato yasa yace." Ki kashe tv haka kije kiyi sallah malama kin kurawa tv ido 'yar kauyen *Dabi."* bata ce masa komai ba ta kashe tv ta nufi bandakin dake dakin alwala tayi ta fito ta tada sallah....Cikin dubara ya mike ya nufi bandakin domin daura alwala. Sai bayan Sallah isha'i sannan Hajiya Fatsima ta iso ita da Baban gida suka gaisa sosai Tana tambayar jikinsa Sayyada tace"Alhamdullahi Tace"Ga kaya na d'ebo miki tunda zaman asibiti ya kamaki Abbanku yace."Ki zauna kiyi jinyar mijinki." Rufe fuska tayi tana dariya....Yace."Mammah wannan yarinyar babu abinda ta iya komai ni nakeyi da kaina ni da cewa nayi ma idan kinzo sai ku koma gida tare." Hjy Fatsima tace"Da idona fa naga yanda yarinyar nan take taraiyayarka haba Sadam! Sayyada na iya kokarinta a kanka." Yace." Mammah ba zaki gane abinda nake nufi amma babu komai ta zauna d'in......"Mamah zan biki mu koma gida." Tafada kanta a 'kasa Cikin mamaki tace"Saboda me zaki bar mijinki ki koma gida Sayyada." Tace"shine baya son zamana a gurin." Hajiya Fatsima tace"To in banda abinki Sayyada ba gashi kinji da kunnanki muna magana dashi ba ya amince ki zauna." Sayyada tayi shiru tabbas da zata iya fitowa mata a mutum da ta fayyace mata irin cin kashin da Sadam! yayi mata tsakanin jiya da yau amma babu komai zata zauna kamar yanda ta bukata. Sulaaim da Alhaji Auwal ne suka shigo tare duk bakin gadon da yake kwance suka nufa suna dubashi Sulaiman ya saki fuska sosai kamar ba dazu suka gama fad'a ba shi kuwa gogan naku da yake bai iya 'boye fushinsa ba ai ko kallo Sulaiman bai ishe shi ba. Sai kusan karfe tara na dare suka tafi bayan tafiyarsu da minti biyar dr ya shigo domin dubashi Yace."Yallabai yana da kyau kaci abinci kasha magani ka kwanta ka huta gurin mikin nan har yanzu baiyi mana yanda muke so ba kana yawan motsa gurin." Yace."Kar kadamu Dr zan kwanta yanzu." Dr Ya kalli Sayyada yace."Madam a bashi abinci yaci yasha magani ya kwanta." Tace."Insha Allahu." Dr na fita tayi kwanciyar ta kan doguwar kujera, Sai ta rama abinda yayi mata kuma zai gane tana da rana ko bata da rana a gurinsa. "Ke." ya ambata a hankali Sayyada na jinsa tayi banza dashi...."Ke! ya sake fad'a shiru tayi yace."Ko bakya jin abinda dr yace ne? ki bani abinci da magani na kwanta." Zumbura baki tayi ba tare da ta juyo ba tace"Ai kai d'in ba yaro bane kana iya had'a abincin da kanka kasha maganinka tunda dai ciwon bai hanaka kokawa ba ai ba zai hanaka ka zuba abinci ba." Rai a 'bace! yace."Ni kike fad'awa wannan maganar."!? Shiru tayi masa....Ya jima yana mamakinta tabbas yayi sake da yarinyar ta raina shi Kwanciya yayi bai ci abincin ba kuma bai sha maganin ba Sayyada ta kunna shi babu abunda yake so sai ha'kin taba. Wayarsa tayi ringing sau kusan bakwai bai duba ba ballanta ma yaga me kiran, kamar Sayyada ta dinga fada masa maganar da duk tazo bakinta. Ita kuma jikinta ne yayi sanyi ganin ya kwanta bai sha maganin ba sai ta mike tana mutsika ido addau take Allah yasa Captain Habu ya shigi aikuwa Allah ya amsa adduarta shine ya shigo hannunsa rike da ledoji Captain Habu ya shigo dakin tare da fad'in"Ashe bakiyi bacci ba."Tace"Ina jira ka kawo min shawarma ta." Dariya yasa yace."Sayyada bakinki na son cin dadi ne ko." Tana murmushi tace"To waye baya son dadi." yace."To gashi a ciki lafiya." ledojin ya mika mata ta kar'ba tana godiya shi kuma isa bakin gadon Sadam! "Aboki ya jikin ."!? Alhamdullahi ya fad'a a cunkushe Habu ya samu kujera ya zauna yana masa hirarar abunda ke faruwa Kano suma 'yan boko haram! d'in sun addabesu labari ya samesu cewar an kama wani a cikin Unguwar Ja'in ya shiga a dai-dai ta sahu da bomb a jikinsa. Sayyada tace" Wallahi Yaya Habu ina tsoron mutanan nan Allah yasa kar su shiga Garinmu." Habu yace."Insha Allahu Allah xai kawo mana karshen matsalar nan, za muyi maganinsu da yardar Allah." Hira suka cigaba da yi tsakanin Sadam da Habu akwai shakuwa da yarda da juna shiyasa duk wani abu da ya danganci Sadam! din Habu yake shiga ciki yayi kane kane Yace."Dazu kafin in shigo Halima ta kirani ta sanar dani abunda ya faru da kai da ita kaga irin abinda nake guje maka ko.......Sadam! yace." Don Allah ka rabu dani da zancan wata Halima itake wahalar da kanta saboda tsabar bata da hankali wai magana takeyi min yaushe zan aureta." Habu yace."Shiyasa naso ka fad'a mata tun tafiya ba tayi nisa ba yanzu sai da ka bari ta sakankance zaka aureta sai kace wani abu hakan bai dace ba" Tsaki yaja yace."Habu bafa zan auri yarinyar da tasan wani namiji ba a waje kasan ni ina da kishi ina zargin Halima da bin maza shiyasa sam ban sanya ta a raina ba." Habu yace."To Allah ya za'ba abunda yafi alkairi Sayyada na jinsu suna magana ba tace komai ba kazar ta takeji tana kur'bar yoguht.....amma duk jikinta yayi sanyi da jin labarin Halima.......Tana jin yana ambaton sigari ta kalleshi Captin Habu yace."Ni bani da ita yanzu...Da sauri tace"Yaya Habu kar ka bashi abinci da magani Dr yace yaci yasha shine ya kwanta." Yace."Ashe baka ci abinci ba."? Daga kai yayi alamun Eh. Habu yace." To ai laifinki ne Sayyada kece ya kamata ki bashi abincin yaci ki bashi magani." Tura baki tayi tace"Yaya Habu shine fa yace bani da amfani a gurunsa dani da babu duk daya shine na barshi yaci abincin da kansa." Habu yasa dariya yace."Lallai Sayyada baki san waye Sadam! ba idan zaki dinga saka maganganunsa cikin ranki zakiyi ta damuwa mijinki wani irin baud'addan mutum ne."! Shiru tayi Habu yace."Yanzu dai bari in futa in baku guri sai ki bashi abincin kamar yanda Dr yace amma kar ki sammasa Kazar ki ta amarci ce na siyo miki." Dariya kawai tayi Habu ya kama hanya ya fita Sadam! na binsa da harara shi a ganinsa wannan abun da Habu keyi kamar zubda girma ne ko da yake aigwara habu kan Sulaiman god'ai-god'ai dashi ya dinga wasa da yara kanana. Sai da ta kammala cin abincinta tsaf sannan ta had'a masa nasa a plate ta nufi gadon dashi......"Koma da kayanki ba zanci ba." tun kafin ta karasa ya dakatar da ita.....Sakare tayi da plate din abincin hannunta....Ya mike a hankali ya isa inda abincin yake ya zubo wani ya dawo ya zauna yana ci da cokali...Jiki a mace taje ta aje na plate din ta nufi bandaki wanka tayi ta wanke bakinta ta fito daure da zanin atamfar jikinta duk ta ji'ko gashin kanta yabi lafiyayyar fatar jikinta ya kwanta, ganin a halin data fito ne yasa yayi saurin dauke kansa.....Ashe munafurci ne 'kumbiya 'kumbiyar da takeyi a cikin hijab yana kallonta ta kasan ido ta dauko karamar rigar bacci iya cinya ta sanya ta daure gashinta ba tare data sanya hijab din ba ta kwanta kan kujera tare da mi'ke santala santalan cinyoyinta.....Duk sai yaji abincin ya fice masa daga rai! ya aje plate din kan drowar ya mike a daddafe ya iske Firji ruwa ya dauko ya koma ya zauna. Sayyada kam bacci ne ya dauketa mai nauyin gaske.......Lalacewa yayi gurin kallonta burinsa kawai yaji jikinsa na gogayya da nasa yana mulmula 'yan 'kananun nonuwan dake gigitashi! tashi, Cikin tsananin sha'awa ya mike ya isa inda take kwamce tsayuwa yayi a kanta ya rasa ta inda zai fara....."Ke! ko bakya jine."!? abinda ya iya cewa kenan Shiru bata motsa ba ya tsuguna tare da tsirawa fuskarta ido hannu yasa ya shafe le'bunanta da gefan fuskarta ajiyar zuciya ya sauke me zafin gaske! a gaggauce ya d'ora bakinsa kan nata yana tsotsar lebunanta yana lumse ido kamar wanda ke shan alawa haka yake ji hannu yasa yana shafa gashin kanta......A firgice ta tashi tana zare ido sai ta ganshi a gurfane a gabanta yayi tarmazai! dashi yana kallonta da fitunanun idanunsa....Le'banta ta shafa taji danshi ta kalleshi a tsorace!!!!! Mur! yaci yace."Ke dallah! tashi ki cire wannan kayan na jikinki sunyi tsaraici da yawa." Cikin alamun bacci tace"To ni zafi nake ji kuma bana iya kwanciya da manya kaya ko a gidane." Yace."Me yasa jiya kika kwana dasu."? "Ai sannan Mammah bata kawo mun wasu ba shiyasa.....Mikewa yayi yana cijewa yace." Tashi ki koma inda kika kwanta jiya." "Um!um! ni ka kyaleni anan nafi jin dad'i jiya a takure na kwanta.'' Kafad'a ya d'aga kamar bai damu ba nan kuwa so yake ta kwanta kusa dashi ko ya samu ya lallatseta. komawa yayi ya kwanta yana tunanin mafita mutukar fa idanunsa nayi masa tozali da yarinyar nan haka to tabbas za'a haifi dan da ba zani kawai sai ya kashe fitila dakin yayi duhu....Ita kuma ta razana da sauri ta mike ta nufi gadon tana lalu'be hannunta ta d'ora a gabansa ya sauke wata wahalalliyar a jiyar zuciya jijiyar ta sake mikewa Da sauri ta cire hannunta daga kai tana mamakin abunda ta ta'ba!! Yaya Sadam! kana ina ne." tafada a tsorace. shuru yayi mata shi kad'ai yasan halin da yake ciki sakamakon d'ora masa hannu da tayi a joystick dinshi........ *Muje zuwa guys* *Maraba da masoya na kwarai lale marhabun da 'yan amana! yau na gama Free peges da yarda Allah me bukata sai ta biya kudin karatu bana mallaka ba, ina neman 'yan amana ne masu bukatar cigaba na bana so ki zo ki biya kudin littafin nan ki futar min dashi idan kinyi haka kin zalince ni kin shiga hakkina kuma wallahi ban yafe miki ba, ke kadai na yarjewa ki karanta tunda ke kika biya kudi me so ta biya ta karanta babu lallai babu dole mutukar dai kikaga littafin kika karanta baki biyani ba to Allah ya isa ban yafe ba🧐* 14/6/2020 *BINTA UMAR ABBALE* _*Littafin Ni da Yaya Sadam! na kudi ne 1_2 #400 ga masu bukata zasu tura kudin ta wannan accont din......0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars zan fada mata yanda zata biya kudin....08089965176 _07084653262.......Mutanan Nijar idan kuna bukata to zaku tura dala dari ta wannan numbar....9089976 _88137740 katin airtal ko orange Dala dari uku kudin Najeria.*_ *NI DA YAYA SADAM!!* 👫👫 *NA* *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌍MANAZARTA* *WRITES ASSOCIATION🖊📚* *M.W.A* _'Kungiya d'aya tamkar da dubu, masu nazari da aiki da Iliminsu burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma nishad'antar da masoyanta._ __________________________________ *Attention⚠️* _*Kada ka/ki biya wani kudin wannan littafin Mai suna Ni da Yaya Sadam! idan kana bukata to ka nemi me wannan numbars itace ainihin marubuciyar littafin......08089965167 _07084653262 Ga numbar da za same ni Ga mai bukatar karanta novls dina*_ *Nana Khadija* *Yaro da kudi* *Gimbiya Balaraba* *Babban yaro* *Mashahuri* *Ladidi kwadaga* *Sadauki Omar* *Tsantsar butulci* *Ruwan dare* *Ni da Yaya sadam!* Ana iya samuna da wad'ancan numbars din nawa dake sama insha Allah xaka samu cikkakun litattafan....Mutukar ka biya kudinka. *Masu Siyar mun da books Ban yafe ba⚠️* *BINTA UMAR ABBALE*