NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE" GAWURTATTU UKU DAGA ALƘALAMIN BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI MARUBUCIYAR LITTAFIN NA FAƊO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA (LABARIN SHANONO DA OGA KAILA. NA SAKE DAWOWA DA WANI LABARIN MAI ƊAUKE DA DARASI, DA BAN TAUSAYI, SADAUKARWA, TSAGWARON ZUNZURUTUN SOYAYYA DA ƘAUNA, FARIN CIKI, BAƘIN CIKI DUK A CIKIN WANNAN LITTAFI MAI SUNA A SAMA. KU BIYONI KU SHA KARATU. ALƘALAMINA BAYA RUBUTA ABINDA BAZAI AMFANAR DA AL'UMMAR ANNABI BA. KAMAR YADDA NA SABA WANNAN LABARIN SHIMA YA FARU A GASKEN GASKE, KU BIYO NI DA HANKICI DOMIN SHARE HAWAYEN DA ZASU ZOBO A GURABEN IDANUWANKU. KU GYARA ZAMA DA KYAU KU BI LABARIN SANNU_SANNU ZAKU FAHIMCI INDA YASA GABA. Lamba ta 1 JIHAR KANO: Kano na ɗaya daga cikin manyan birane a ƙasar Hausa. Kano itace cibiyar kasuwanci ta Najeriya gaba ɗaya. Jihar ta Kano tana da ƙananan hukumomi guda arba'in da hudu. Kana gari ne da yake da masarauta mai ɗunbun tarihi, mai kwarjini a cikin kasashen Hausa da kewayenta. Haka zalika Kano gari ne babba wanda mazauna cikinta ke magana da harshen Hausa. Itace gari mafi yawan jama'a a Najeriya baki ɗaya. Kanon ta yi suna wajen kasuwancin da ta bunkasa a kai, har ya zamana ana cewa da ita Cibiyar Kasuwanci. Haka kuma tarihin Kano ya nuna daman can tana da suna wurin cinikayya tsakaninta da mutanen gabas ta tsakiya. Yawan mutanen da suke garin na Kano sun haura kimanin mutane miliyan goma (10.000,000) a ƙidayar da aka yi a shekara ta alif dubu biyu da shida. Jihar Kano tana da matuƙar tasiri a yawan mutane Najeriya, saboda ita ce ta fi kowacce jiha yawan mutane daga ko'ina a faɗin duniya, tun daga na kudancin Najeriya, har zuwa ƙasashen dake maƙwabtaka da Najeriya,hakq kuma za ka tarar da mutanen sin ( wato china) da kuma na ƙasashen larabawa har da turawan yammacin duniya mutanen Kano sun shahara wajen addini sosai. ƘOFAR MATA. Cikin wani layin masu rangwamen arziki na shiga. Duk da kasancewa safiya ce sosai. Hakan bai hana ganin yara suna kai kawo a cikin unguwa ba. Wasu suna kan layin siyan ƙosai, wasu suna kan layin siyan fanke. Wasu yaran da gasarar kokko na gansu a hannunsu. Kasancewar baifi ƙarfe bakwai da rabin safiya ba. Anata hada_hadar shirin karya kumallo. A bakin wani madaidaicin gida na tsaya marar fenti, mai ɗauke da ƙatuwar bishiyar durumi a ƙofar gidan ƙosasshiyar gaske. A ƙarƙashin wannan bishiyar na hango motoci biyu a fake, ɗayar golf 3 ce, ɗayar kuma Vectra ce. Da dukkan halama motocin ta masu gidance. Wani matashine ya fito daga gidan hannunshi riƙe da bokitin ƙarfe cike dumbul da ruwa, ga soson buhu a ɗayan hannun nashi. A gaban motocinnan ya ajjiye bokitin, nan take ya soma watsa ma Vectra ɗinnan ruwa. Daga cikin gidan dai na jiyo hayaniya na tashi kuma muryar namiji nake jiyowa, har da kukan mace daga bisani na jiyo. Ba shiri na faɗa cikin gidan dan ganin meke faruwa haka. Abun mamaki ashe gidan babbane sosai daga ciki, gashi da yalwar tsakar gida. Ɗakuna kuwa gasunan a jejjere kamar a zangon baƙi ( Hotel). Maza da matan gidan, harma da yaran gidan na tarar a tsakar gidan. Wani babban mutum na gani yana ta faɗa, muryarshi ce take fita har ƙofar gida. Babbane a shekaru, dan har da furfura a gemunshi da sumar kanshi. A gefenshi na hango wata doguwar fara kyakkyawar mace a tsaye jikinta sharkab da ruwa har ɗiga take yi tsabaragen jiƙewa, kuka take yi ƙaƙas tamkar wacce akayi ma mutuwa, gata ita dai ba yarinya bace. Wannan Dattijon cikin murya mai amon ɓacin rai yace. "Haula ki dena kukan ya'isa ki bari su fito inji in shi Gwadabenne yasa matar tashi ta watsa miki ruwan kashi sai in ji. Ke da gidan mijinki babu wanda ya'isa ya takura miki wallahi, zan ture zumunta in kori Gwadabe da iyalinshi a gidana, wannan ƙazanta ta buskuta samodarar matarshi ni ya isheni. Ina mai takaici da baƙin cikin haɗa zuriya da matar Gwadabe da mu ka yi" Ya ƙarashe maganar yana huci kamar zaki." Gwadabe:. Da sauri ya fito daga ɗakin nashi rigarshi a hannu, shimi ce a jikinshi da koɗaɗɗen wandon jeans wanda akayi ma wanki sama da sau saba'in, duk yayi yaushi, ya sake kala daga turarren bulu, izuwa kalar sararin samaniya. "Yaya Hambali kayi haƙuri dan Allah. Kema Yaya Haula ki yi haquri. Iyabo ba da saninta ta watsa miki ruwan kashi a jiki ba. Bata san kina banɗakin bane, amman kiyi haƙuri dan Allah, kuma zata kiyaye " Gwadabe ya faɗa cikin sigar kare iyalinshi, duk da abinda ya faɗan gaskiya ne. Amman dake a hasale suke da Iyabo shi yasa maganar take ƙoƙarin zama babba. Dama ƙiris suke jira ta kuskure su dirar mata a wuya, sabida tsantsar ƙiyayyar da suke nuna ma Iyabo wacce har idanuwansu suka rufe wannan ƙiyayyar tashafi ɗan uwansu gudan jininsu Gwadabe. Harisu wanda ya kasance wa ga Gwadabe, ƙani ga Hambali, ɗa na uku a wajen mahaifiyarsu yace. "To ita shafaffiyar da mai bamu da matsayin da zata iya fitowa ta ba Yaya Hambali da Yaya Haula haƙuri kenan ko yaya akayi ne Gwadabe?. Nifa na kasa gane wannan baƙin sha'ani naka da iyalinka kanka kalau yake kuwa" Yaya Hambali wanda maganar Harisu ta kasance tamkar zuga a gareshi yace. "Ta fito ta ba da haƙuri kuwa Harisu? alhalin ba ganinmu da gashi take yi ba. Gwadabe ya gama watsar mana da darajarmu a idanunta. Allah wadaranka Gwadabe ka cucemu daka cakuɗa mana iri da Iyabo, ba zamu taɓa yafe maka cutarwar da kayi mana ba." "Ya'isa haka Yaya Hambali dan Allah mana. Wannan maganganun tamkar cin fuskane a wajen Iyabo. Sannan ni banga aibu ko laifin Iyabo dan ta kasance Beyerabiya ba. Ni da ku, da iyabo duk musulmaine,kuma duk mutanene Allah ɗaya muke bauta ma, kuma kamar yadda muke sallah, da azumi haka take yi itama" Azabure Hambali yayi kanshi a zafafe yana shirin dukan ƙirjinshi. Harisu ne yai musu iyaka ta hanyar shiga tsakiyarsu dukan ya sauka tabb a tsakiyan gadon bayan Harisun tsabar zafin dukan saida ya gantsare. Jikin Yaya Hambali har rawa yake yi yana ganin Gwadabe kamar yayi mishi rashin kunyane. Barinma yana ganin Gwadabe tamkar shi ya tsugunna ya haifeshi tsabar girme mishi da yayi. Mutum huɗu ne a tsakaninsu kafin Gwadabe. Akwai Yaya Halima wacce ta kasance itace Babba a cikin ummansu, sannan shi Yaya Hambalin, ga Harisu, sannan ga ɗan Fodiyo, ga Sukairaju. Shi Gwadabe daga shi sai Da'u, daga Da'u sai Zakari, sai ƴar Auta Sauwama." Shi kanshi Gwadaben har cikin ƙoƙon ranshi baiji daɗin yanda yayi ma Yaya Hambalin ba, ko babu komai ya girme mishi, kuma shine makwafin uba a garesu baki ɗaya, gashi cikin ummanshi. Yaya Hambali ya bauta musu sosai, kasancewar tun suna ƙananu Allah yai ma mahaifinsu rasuwa. Shi ya maye musu gurbin uba, shine noma, shine kiwo, Fataucin dabino kuwa shi ya gaji mahaifinsu, yayi musu dukkannin wani gata har Allah ya cicciɓesu suka kai matakin mallakar hankali da girman jiki, dana haihuwa. "Lallai Gwadabe baka da hankali ba'acikin hayyacinka kake ba, matarka da danginta sun gama mallakeka, imma ka yarda, imma ka ƙaryatani, tunda ka soma sa'insa damu shingin duka ya rage.Yaya Hambalin kake mayarma da magana?" Cewar Ɗan Fudiyo wanda ya cike da mamakin ɗan uwan nasu Gwadabe" Yaya Hambali kuwa tsai yayi yana kallon Gwadabe, tare da ƴan uwanshi da suka dira mishi a ka, kowa na tofa albarkacin bakinshi a kan abunda matarshi Iyabo ta yi, da abunda ya aikata yanzu. Gabaki ɗaya Gwadabe sai ya dibibice, kasancewar ba halinshi bane raina na gaba an yi mishi wannan kyakkyawar shaidar sosai. Ya fusata ainun ne da yanda suke cin zarafin iyalinshi ba dare ba rana, ba tare da ta yi musu laifin zaune ba, balle laifin tsaye. ana cikin haka Sai ga Iyabo ta ƙaraso wajen a kidime, jikinta har rawa yake yi dan tasan Gwadabe ba karamin ruwa ya kirawo mata ba" Iyabo:. Tunda Gwadabe ya fito jikina yake ɓari, domin nasan danginshi kab ba ƙaunata suke yi ba, kuma ƙiris suke jiran kuskure na. Sai gashi yau azal ta hau kaina. Daman daren jiya cike na kwana da fargabar zuwa ƙauyansu Gwadabe da zamu je yau biki. Ina tsoron Allah ina tsoron abinda zai haɗa taron biki, ko suna a ƙauyensu Gwadabe ace kuma zanje nima. Ina muzanta, da takura fiye da tunani. Furucin da Gwadabe ya fesarma da Baban Nazifi ya fi firgitani fiye da dalilin rikicin. Ba shiri na buɗe labule na fito ina tura tsohon cikina gaba. Saye nake da leshi riga da zane. Rigar ɗinkin buba, zanin kuma ciki da alako irin ɗinkin yarenmu kenan. Idanu mu ka haɗa da Gwadabena tausayinshi ya sake dirarmun a zuchiyata, har nake jin ko ratayeni danginshi zasu yi, ni da Gwadabe mutu ka raba. Dan shi ɗin cikakken jarumin masoyine na haƙiƙa tunda ya aureni bai sake samun kwanciyar hankali da salama ta ɓangaren iyaye da dangi ba. A zamantakewata dashi kuma haƙiƙatan bai taɓa yi mun wani abun ashsha ba, riritani yake yi, gami da tarairayar zuchiyata tamkar ƙwai, hakanne yake ƙaramin ƙarfin zuchiya da jumurin shanye duk abinda danginshi suke yi mun. Sai dai irin zaman bashi da daɗi, yana raɓa rayuwata da dukkannin farin cikina. Damma Gwadabe na ƙoƙarin sharemun dukkan hawayena. Dan Allah Baban Nazifi kayi haƙuri. Umman Nazifi dan Allah ki gafarceni wallahi bansan kina cikin banɗakin bane, ban watsa miki da ganganba" Na faɗa ina mai ƙoƙarin haɗiye kukana tare da shanye fishina. Idanu Gwadabe ya lumshe mun cikin sigar ban haƙuri, nima nawa idanun na lumshe mishi cikin bashi amsar shima yayi haƙurin. Idanunshi ya rufe ya buɗesu tare da ɗan zare su, halamar ya samu sassauci a zuchiyarshi. Dukkan wannan maganar kuramen masoyan dake gudana a tsakaninmu babu wanda yasan me muke nufi, amman dai suna kallonmu, idanun kowa a kanmu yake. "Ke Iyabo kar ki sake zubar mana da kashi ta magudana, nan ba gidan yarbawa bane, dama ku yarbawa a cikin ƙabilu wama ya kaiku ƙazanta, da ɗaukar kashi ba abun ƙyama ba?. In banda ƙazanta yama zaki zubar da kashi ta magudana. Mu dai ana cutar damu da wannan kafirar ƙazantar ta yarbawa." Cewar Gude matar Yaya Sukairaju Kenan. Dama tafi kowa tsanata da caccaɓa mini maganganu kaifafa. Na ji zafin abinda ta faɗa a kan yarbawa, dan ina kishin yarena ina kuma alfahari da kasancewata Beyerabiya." "Gwadabe da mun dawo daga Takai biki ka tattare matarka da ɗanka ku bar mun gidana, na gaji da ganinku dukkanku." Da sauri na dubi Gwadabe, shi kuma ya kalli Baban Nazifi. Ba mu kaɗai mu ka jijjiga da furucin Baban Nazifi ba, sauran yayyen Gwadabe da matayensu, harma da yaransu wanda suke fahimtar abunda akeyi sai da su ka girgiza. "Haula mu je ki sake kayanki mu kama hanya banso takwas ta yi mun a gida ba. Sukairaju ku kama hanyar tafiya muma yanzu zamu kama hanyarmu" Take kowa ya watse ya barmu jijjunanmu a sanyaye sosai. Hannuna Gwadabe ya ja a hankali mu ka koma ɗaki. Muna shiga na zauna a kujera daɓas sai da kujerar ta yi ƙara kasancewata mai ƙiba da ɓaka_ɓakan mazaunai. Kuka mai gunji na fashe dashi. Gwadabe ya zauna a kusa dani ya dafe kanshi da hannu bibbiyu, idanunshi yayi jawur. Ya kasa furtamun kalma sai tubka da warwara kawai yake yi, tare da neman tudun dafawa. Mu da mu ke cin abinci da wuya ta ina zamu iya kama hayar muhalli? Dama dai burin dangin Gwadabe su ga mun tagayyara ne yau na sake tabbatarwa. "Ki yi haquri Iyabo da duk abubbuwan da kike gani, kike ji, da wanda zaki sake ji in mun tafi Takai. Ina mai ƙara baki haƙuri kuma ki sani ni Gwadabe ina tare da sonki, ina sonki Iyabo fiye da son da uwa take ma ɗan cikinta. Ina mai baki haƙuri Iyabo bisa abinda dangina da naki dangin suke yi miki duk sabida Aurenmu. Ina alfahari da soyayyar da ni Gwadabe nake yi miki. Wallahi Iyabo kece sanyi da farin cikin ruhina. Ki share hawayenku mu kama hanyar Takai Sukairaju ya ɗakko mana bus zamu tafi baki ɗaya." Hawayena na share jikina a mugun mace murus, kalaman Gwadabe sun kashe mun jiki. Haƙiƙa Gwadabe na yi mun soyayya mai yawan gaske. Amman ko ƙafar inda nake son shi bai kama ba, gashi a kullum zuchiyata sake jarabtuwa da Gwadabe take yi. Gwadabe yanzu in Baban Nazifi yace mu bar mishi gidanshi wanne tudu zamu dafa, ina zamu bi mu ga haske? Ka duba ka gani abinci da ƙyar muke ci. Wanke_wanke da sharar da nake zuwa yi albashin nera dubu biyu ne a wata, kuɗin ba yawa bane dashi. Kai kuma ba ko da yaushe oganka yake samun lodi ba balle mu samu ɗan kuɗin sallamar iyali da ake baku. Gwadabe ya zamu yi dan Allah?" "A'a Iyabo Allah zai yi mana mafita. Zamu tattauna maganar a gaban Babala in mun je Takai. In ta goyi bayan Yaya Hambali kan mu tashi mu bar mishi gidanshi. Ba makawa zamu tashi duk da nasan bani da ko ficikar da zan iya kama mana haya. Dukkanmu a ƙasanta mu ke tunda ita ta haifemu, kinga tsohon ciki gareki damuwa da kuka ai ba naki bane ƴar yarbawata. Oh Allah yayi ba Debisi bane mijinki, ni ɗin dai da basa so ni na yi sa'ar samun ki, Alhamdulillah. Ko mutuwa na yi nasan na zaɓarma yarana uwa ta gari, ba zasu tuhumeni ba." Dariya nayi harda ƙyaƙyatawa, shima dariyar yake yi. Muka shiga tuno gwagwarmaya da muka sha kafin mu kawo wannan matakin. Duk da dai har gobe tsugunne bata kare mana ba. Tuni nasa ƙafa na shure matsalolin dangin Gwadabe na miƙe na shiga ciki dan ɗakko mana jakar kayanmu. Toye yana kwance sai baccinshi yake yi a shirye yake tsab. Mayafi na ɗauko na jawo ƙaramin akwatin kayanmu da jakar kayan Toye. Ni banso tafiya ma dashi ba naso in Kai shi gidanmu, sabida nima fama nake da kaina cikina wata bakwai amman girmanshi yasa ake mun kallon haihuwa ko yau ko gobe. Toye shekararshi shida da haihuwa sa'anninshi na gidan duk sun shiga makarantar islamiyya mu bamu da kuɗin saka shi a makaranta, in yaje ma ana koroshi kuɗin laraba, inna samu ko ni ko Baban sai mu biya. Amman da zaran laraba tayi bamu biya ba ake koroshi, sai Gwadabe ya yanke hukuncin ni na dinga koya mishi Abacada, Gwadabe kuma yana koya mishi baƙin arabic. Shigowa yayi ya saɓa Toye a kafaɗarshi ya zari akwatin kayanmu. "Zaki iya ɗaukan jakar kayan Toye ko in kai wanna in dawo?" Murmusawa nayi na ɗauki jakar kayan da jakar hannuna, na bi bayanshi. Gaba su ka yi, ni kuma na tsaya na kulle ƙofata na biyo bayanshi. Da ƙyar fa nake tafiya gashi duk na yi kumburi, ga hawan jini na masu juna ina fama dashi. Ko da muka fito, sai muka tarar Bus ɗin ta cika duk sun ɗaura yaransu a kan kujerar sun babbake. "Motar ba zata isaba Gwadabe abinda za'ayi ku je ku hau motar haya zaifi." Cewar Sukairaju yana gama faɗar haka suka ja motar fu, Bus ɗin na gaba motar Baban Nazifi na biye, kana motar Harisu ta rufa musu baya. Yawu Gwadabe ya haɗiye muƙut jijiyoyin kanshi suka fito raɗa_raɗa. "Mu je tasha Iyabo" A daƙile yayi maganar. Ni kam ina biye dashi ko gani bana iya yi sosai tsabaragen tashin hankali da damuwa. Shikenan na yi sanadiyyar raba kan wannan zuriyar masu son juna da son zumunta? Gwadabe tunda ya aureni ya zama saniyar ware a dangi. Ina jin rashin daɗi da na zame mishi silar zama mujiya a cikin dangi. Har mu ka isa tasha banji Gwadabe ya ce komai ba, hakan ya sake damuna ainun gashi muna hanya babu damar in rarrasheshi ko zai samu ɗan sassauci. Ga wani ruguntsumin ma yana jiraye damu a Takai. Mota ya sama mana Bus ni da shi ne a can baya ta ƙarshe wajen window, Toye yana rungume a jikinshi yana baccinshi. Yaron na ƙura ma idanu ina mai cike da tausayinshi da abunda yake cikina ta yanda zasu rayu cikin rashin gatan dangi ɓangaren uwa da uba, Toye ko cikin yaran gida ya shiga bashi da damar yin wasa dasu, yaran zasu shiga yi mishi waƙar da iyayensu suka saba rerawa a tsakar gidan. Suna tafi suna cewa Yarbawa masu kwalo_kwalo da ɗuwawu suke tuƙin tuwo. Toye sai yai ta kuka abunka da yarinta, wataran ma da gudu yake dawowa ya faɗa jikina. Ta bangaren dangina ma suna adawa da aurena da Gwadabe sosai da sosai kasancewar shi Bahaushene ba Beyerabe ba. Rabon ƴaƴane da ƙudurar Allah ya tabbatar da aurena da masoyina Gwadabe. "Tunanin me kike yi haka Iyabo mai zurfin gaske. Kaddai akan furucin Yaya Hambali ne akan mu bar mishi gidanshi? Iyabo ni kaina inaso mu tashi a gidan ba tun yau ba. Ko dan kema ki samu yancin yin rayuwar ƴanci irin wacce ko wacce mace take fatan samu. Na yi imanin dangina ba zasu zo har gidanki su takura miki ba, ko zasu takura miki ba kamar in gidanmu ɗaya ba. Ni da na zame musu dole zanyi zumunci dasu..." A'a Gwadabe wannan ba zai ma yiwu ba. Babala ba zata bar Baban Nazifi ya tozartamu ba. In muka bar gidannan ina zamu shiga a ina zamu dinga samu kuɗin da zamu biya haya? Sannan yarannan zasu sake rasa dangin mahaifansu ta dukka ɓangarori biyu. Amman in dai muna taren a gida ɗaya su Toye zasu taso da sanin lallai su Nazifi ƴan uwansu ne danginsu ne, a gida ɗaya akayi tarbiyyarsu. Kar ka mance Babala ma burinta kenan ganin kun haɗe kawunanku da na iyalinku baki ɗaya. Ka yi haƙuri da batun tashinmu,madamar ba Babala bace ta goyi bayan Baban Nazifi akan tashin namu ba. Kasan sai ka ƙara mun baƙin jini a wajen danginka" Idanu ya lumshe kawai sai girgiza kanshi yake yi. Ɗan guntun siririn hawayen daya surnano mun na yi maza na share gudun kar Gwadabe ya buɗe idanunshi ya ga zubar hawayena. Har Bus ɗinmu ta cika muka fito daga tasha bamu sake magana ba. Ko wanne cikinmu aikin tubka da warwara kawai yake yi a zuchiyarshi. Motarmu sai gudu take shararawa bisa titi, tun muna wuce titinan cikin gari muna wuce manyan gidajen sama, da manyan shopping mall har mu ka soma wuce ciyayi da fasassun kwalta, jagab_jagab ɗin hanya ne yasa Gwadabe yai ta mun aikin sannu har muka shiga cikin ƙaramar hukumar Takai. TAKAI TA KAWO TA SABA DA SAUKAR BAƘI Takai ƙaramar hukumace take jihar Kano. Yanki ne wanda Allah ya albarkace shi da ruwan sama a sanadiyyar hakanne mutanen yankin su ke noma da kiwo da kasuwanci gashi Allah subuhanahu wata ala ya albarkaci garin takai da bishiyun dabinai masu yawan gaske, dabino ya wadaci jama'ar Takai sosai mota_mota ake fita da dabino domin kasuwancinshi. Garin Takai yankine wanda ya yi nesa da birnin kano da tsawon kilomita 80, yayi kusa da yankunan ƙasar Bauchi, yankin da yake yawan kawowa ƙasar kano farmaki a lokacin sarkin kano (Babba Zaki) Sanadiyyar hare_haren da yake yawan kaima birnin kano, Sarkin Kano Babba Zaki ya yanke shawarar a kafa ƙasar Takai, kuma ayi ganuwa a garin. Hakanne yasa ya tura mayaƙa domin su zauna a garin. Bayan an kafa dausayin yaƙi a garin Takai, Sarkin Kano Babba Zaki ya gina gidan sarkin kano a garin Takai kuma ya so ya koma garin Takai ɗin da zama." Muna sauka daga mota mu ka hau mashin ya wuce damu Unguwar Dibinai unguwa mai dogon tarihi kenan a garin na Takai. Dai dai ƙofar gidansu Gwadabe acaɓanmu ya tsaya, ƙofar gidan cike maƙil da maza, mata kuma sunata shige da fice. Bara'u Abokin Gwadabe ne ya tarbeshi da fara'arshi, yasa hannu ya amshe Toye ya rungume. "Madam Iyabo barka da isowa tsuntsun soyayya" Dariyar dole na yi mishi, dan muddun muka haɗu dashi sai ya furta wannan suna daya raɗa mana. Bara'u barka dai da gida, ya yara da Sakinar?" Dariya yayi yace. "Sakina tun safe tana cikin gida sun zo taya aikin biki. Yaran naku ma zaki gansu a ciki" Ɗan murmusawa nayi, Gwadabe ya dubeni yace. "Iyabo ki shiga ciki, zan gaggaisa da ƴan uwa da abokan arziki. Gasu Yaya Hambali can a ƙarƙashin bishiyar dabino suma " To shikenan sai mun haɗu, ka kawo akwati da jakar to" Dan nasan matsawar ban karɓa ba da ƴan uwanshi sun ƙilla ido suka ga akwatinan a hannunshi to zan sha habaici da maganganun banza" Bara'u yace. "Bashshi ki yi fama da kanki, yara zasu shigo miki dashi" Gwadabe yace. "Kaima ka faɗa mata, da ba dan bikinnan ya zame mata dole zuwanshi ba, ai da bama zata yi doguwar tafiya da ciki haka ba, baka ga wuyar da tasha a hanya ba wallahi. Bikin Auta guda in bata zo ba kai kasan akwai ƙura" Ni dai a wajen na yi shigewata cikin gidan na barsu a tsaye suna tattaunawa, Gwadabe bashi da aminin daya shallake Bara'u a wajenshi, tare suka taso, su kai wasan ƙasarsu, har shayi tare akayi musu. Komawar Gwadabe Cikin birni bai rage amintakarsu ba sam, dan Sakina matarshi tasha zuwar mana ita da yara, sai su fi sati biyu. Nima dolena in na zo Takai a gidan Sakina nake sauka. Zuwana na ƙarshe wanda daga shi ban sake zuwa ba sai yau ne kawai Babala tace bazan sauka a gidan Sakina ba, a cikin gida zan zauna, kuma ta kafa dokar ta haramta mun zuwa gidan Bara'u in kwana, ba dan komai ba sai dan a sake ƙuntatani. Gwadabe:. "Gwadabe lafiya irin wannan ramar da kayi haka?" Cewar Bara'u wanda ya kasa haƙuri sai da ya ja Gwadabe gefe dan su ɗan zanta,bayan ya bi mazan dake ƙofar gida an gaggaisa. Gwadabe ya girgiza kai yace. "Wallahi Bara'u kai kasan komai al'amuranne sai godiyar Allah kawai. Kasan in akace maka magidanci bashi da cikakkiyar sana'ar kanshi dole hankalinshi bazai kwanta ba. Karen mota nake yi har yanzu dai daka sani. Amman muna sa ran za'ayi mana freedom da yardar Allah muma a bamu mota, in hakan ya tabbata za'a samu sauƙi. A hakanma ban fa zauna ba, buga_buga akeyi babu dare bare rana, muddin akace maka safiya ta yi, to fa in na fice duk abunda na samu yi nake yi. Nine kwashe shara, nine kwashe kwata, nine bin masu Bus na zuwa unguwanni ina karen mota. Kaga duk sana'oene na cin abinci kawai, abincinma bafa sau uku a rana ba. Duk ranar data carke wallahi sai dai in tura Iyabo gidansu ita da Toye dan su samu abunda zasu kai bakin salati, haka iyayenta zasu ci mata mutuncinta in taje musu, to amman ni hakan yafi mun. Ni kuma haka zan wuni neman aikin yi. Babban abunda yake sani cikin juyayi shine a wannan halin da muke ciki ko Bara'u? To Yaya Hambali, da su Sukairaju, Fodiyo, Yaya Harisu kai dukkansu. Su a wadace suke da abinci, dan Yaya Hambali kullum da nama ake miya a tukunyarshi. Ni kuma na sama raina in yinwa ita zata zame mana ajali ni da iyalina sai dai mu mutu. Bara'u bazan sake tambayar tallafi ko taimako a wajen kowa ba. Wulaƙanci wanne ne ni Gwadabe ban gani ba? Yanzu nan yau Yaya Hambali yace mu tattare yamanu_yanamu mu bar mushi gidanshi. Dan kawai Iyabo ta watsa ma Yaya Haula ruwan kashi ba tare da saninta ba, fitintinun gidan kaɗai ya'isa yasa in yi rama wallahi." Mrs Bukhari ce Sai mun kasance a cikin wannan kayataccen labarin mai ɗauke da dumbin darasi. Tafiyar tana da tsayi sosai. Ku shirya tsab kafin fitowata Inanan tafe ba da jimawaba in sha Allah 👍🏻 https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Lamba ta biyu Gwadabe:. Numfashi ya ja, tare da jin wani irin turirin zafi a zuchiyarshi. Yana mamakin yanda ƴan uwanshi suka juya mishi baya sabida Iyabo. Bara'u ya ja ajjiyar zuchiya yace. "Wannan ja'iba har yanzu barta ta wuce ba Gwadabe?, Aure sama da shekaru shida, ga rabo a tsakani har yanzu basu sauke aƙidarsu akan Iyabo ba? Naga ma ana wanke Arniya a aureta ba tare da ta bar arnancinta ba, kuma addini bai haka hakan ba, ballantana Iyabo wacce take musulma gabanta da bayanta. Shawarata anan Gwadabe shine ka yi haƙuri ka ba Yaya Hambali haƙuri kuci gaba da zama a ƙarƙashin inuwar dukiyarshi. Kuma nima na mara maka baya kar ka sake ka nuna musu ka gaza akan iyalinka, gara ka dinga turata gidan nasu duk wulaƙancin da zasu yi muku. Gwadabe kai mutumin kirki ne sosai, bana mance alkhairanka gareni. Bazan mance ba lokacin kana samu kai ka biya mun sadakin Sakina, ka siyo mun turamen zani har guda biyar aka zuba a famtimoti banda abubbuwa da kai ta binmu mu abokanka dashi na alkhairi. Kai kayi silar fitan Tamu gada cikin garinnan na Takai ya shiga Kano. Ashe hanyar arzikin nashi kenan yanzu ina Tamu? Yana Habuja shi da iyalinshi, sun samu rufin asiri sosai. Allah bazai hofantar da mutum irinka ba, matsawar kaga ka roƙi arziki Allah bai baka ba Gwadabe ka ɗauka cewar arzikin ƙila ba alkhairi bane a gareka. Kar in cikaka da surutu gara ka shiga ka samu Iyabo, wala Allah dangi su sassauta daga tsangwamarta in suka ga kaifin idanunka." Hannu yasa a ajjihu ya zaro nera dubu uku ƴan muttala_muttala ya tura a aljihun koɗaɗɗen jeans ɗin Gwadabe. "Ka ba Babala gudunmawarka basai kace mun baka dashi ba, ta nuna a jikinka." Hannunshi ya ja suka nufi cikin gidan. Gwadabe sai murmushi yake yi gami da yabon ƙoƙari na Aminin nashi a kanshi. Jifa_jifa Bara'u na yi ma Gwadabe aiken gyaɗar miya, da shinkafa ƴar hausa. Abunda yake nomewa kenan, kuma ƴar gonar tashi ba wata babbar gona bace ga hidindimu masu tarin yawa a kan nashi. Iyabo:. Ƙafafuna har rawa suke yi wallahi dana ɗora ƙafata a cikin gidan. Da Yaya Halima na soma cin karo ta tawo ita da ƙawayenta, taci kwalliya, da halamun rakiya zata yi musu. Dariyar dole na ƙaƙaro nace. Yaya Halima rakiya zaki yi ne. Ina wuni? Na furta da hausar bakina irinta yarbawan da suka ƙware a yaren Hausa. Dan babu kalmar da take bani wahalar furtawa sai dai nakan furtatane da irin Hausar bakina. Harara Yaya Halima ta doka mun, ta ƙura ma titsetsen cikina idanu ƙur. Tsaki ta ja mai ƙarfi suka wuce ni ita da ƙawayenta fuu. Jikina ya sake macewa mus, da jan ƙafa na ƙarasa shiga babban gidan nasu mai ƙofofi huɗu, ko wanne shiyya da ƙofarshi, amman gidan gabaki ɗaya a haɗe yake, ƴan uwane dangin juna da yaransu da jikokinsu a cikin gidan. Babban wan mahaifin su Gwadabe shi ya tara kan wannan dangi a waje ɗaya, kasancewar mahaifinsu Allah ya albarkaceshi da yawan yara (kakan su Gwadabe kenan). Su rai Talatin da uku mahaifinsu ya haifa, matanshi biyu rak. Sai wan mahaifinsu Gwadabe yaji bari ya haɗe kan ƙannenshi su zauna waje guda domin ƙarfafar zumunci. Irin abinda Babala tayi kenan akan Yaya Hambali daya haɗe kan ƙannenshi waje guda suke rayuwa gida ɗaya. Su Baban Nazifi da su Sukairaju kowanne cikinsu yana da ɗakinshi da yake sauka in sabgar biki ta kawomu, akwai katifu da labuleye a ɗakin. Gwadabe ne kawai bashi da ɗakin sauka in mun zo. Hakan ya farune sakamakon ni ya aura ƴar ƙabilar Yoruba bai auri ƴar ƙalibarsu ta Hausa fulani ba. Ina shiga shiyyar Babala naci karo da su Yaya Haula, da Sawaiba matar Harisu, dasu Gude sune ƴan gaba gaban murhu anata tuƙa tuwon jama'ar biki. Duk suka kalleni suka watsar, nasu kam ai na daɗe da sabawa. Ko da nayi sallama ɗaiɗaikun mutanene suka amsani, suma baƙine da suka shigo daga wasu ƙauyukan dan taya iyalan wannan gida murnar biki. A sanyaye na gaishesu har zan wuce Yaya Haula tace. "Ai kamata yayi ki ci ɗamara da mayafinki ki zo ki tuƙa mana tuwonnan yayi sumul kamar Amala, kinsan dai a gidan surukai kike. Cijewa nayi nace mata. To bari in gaisa da su Babala sai in zo Yaya Haula" Shikenan iyakar abunda nace, Sai kawai Gude ta daka tsalle tace. "Lallai Iyabo wuyanki ya isa yanka sosai. Gwadabe ya ɗaure miki kugu sosai. Ke har kina da ta cewa a cikin zuriyarnan, ɗorin dosono dake? Ai da gidanku kika je bikinku na kwalo_kwalo dole ki zage kici aiki dama yarbawa ba'a sanku da hutu ba sai wahala" Hawayen da suke shirin zubo mun nayi saurin mayarwa dan hango Babala tana nufomu. Tana ganina ta zabga mun harara mai muni. Babu shiri na zube a ƙasa ko nauyin cikina banji ba. Barka da fitowa Babala" Tsaki taja. " In Kinga dama kin tashi daga wannan tsugunnon naku na gado. Kin shigo garin amman baki iya zuwa inda nake kin gaisheni ba, balle matan yayyena da ƙannena su ci albarkacina a matsayina na mahaifiyar Gwadabe. Sai da kika ganni zaki wani zube a ƙar, ai ni na ɗauka ba zaki barshi yazo bikin ba ma." Hawaye take ya tsinke a idanuna ya soma zuba shar_shar_shar, in furta kalma na kasa, in ɗago in bata hakuri na kasa bakina yayi mun nauyi ainun. "Haula menene yake faruwa nake jiyo hayaniyarku ne?" Babala ta faɗa cikin ɓacin rai. Abinda Yaya Haula take jira dama kenan ai kuwa sai cewa tayi da Babala. "Ce mata fa nayi tazo ta tuƙe mana tuwonnan yayi laushi irin nasu yarbawa. Shine ta nemi faɗa mun magana Babala, so take ta fake da ciki ta ƙi yin aiki. Lokacin bikin Rahina ma haka ta kwanta jinya ko tsinke taƙi ɗagawa. Ko a can Kano Gwadabe shi ke mata har shara da wanke_wanke, balle kuma wanki da wankan Toye" Baki Babala ta riƙe tana jijjiga kai kawai. "Ba shakka ashe har yanzu Yarbawa suna da baƙar zuchiyar yin agumu. Abunda na dinga jiye ma Gwadabe kenan yaƙi ganewa sabida tun ana neman aka gusar mishi da hankali. Ai sunan Gwadabe ya daɗe a hannun Baba lawo ( Bokan yarbawa)" Hawaye kawai nake zubarwa rana zafi inuwa ƙuna. Ana cikin wannan ruguntsumin Gwadabe ya shigo yana rungume da Toye ga jakar kayanmu yana ja, Bara'u na riƙe da jakar kayan Toye. A tsaye suke suna gaisawa da dangin Babala, amman hankalin Gwadabe na kaina yanda yaga ina tsiyayar hawaye gani a gurfane. Ba shiri ya iso inda muke. "Babala lafiya meke faruwa haka? Iyabo ke ba likita ya hanaki tsugunno ba, tashi tsaye" Ya faɗa a sanyaye. Babala ta sauke gwauron numfashi ta dubi Gwadabe tace. "Babu shakka Gwadabe, sannu me mata. Wato likita ya hanata tsugunno a tsaye kake so ta gaisheni kenan ko marar albarka? Yayi kyau ai ku sha kuruminku komai ma ya kusan zuwa ƙarshe da izinin Allah" Tana faɗar haka ta wuce fu tana share hawaye. Bansan me akayi mata har da zai sata zub da hawaye ba. A kullum naga Babala na kuka akanmu tsorone yake sake shigata dan kukanta a wajen Gwadabe babbar musibace wacce ko arziki bazai bari yayi ba. Gabana ya yanke ya faɗi, take na ji jiri na shirin kayar dani. Me take nufi da komai ya kusan zuwa ƙarshe to? Ko so take Gwadabe ya rabu dani kenan ya auri Bahaushiya ƴar uwarshi?. A baya haka Babala ta tursasa Gwadabe sai da yai mun saki ɗaya. Sakin daya sake rura wutar rikici tsakanin dangina da dangin Gwadabe kenan, wannan saki ba ƙaramin ta da zaune tsaye yayi ba. Dan Iya Debisi da Babala sai da suka kusan raba abun faɗe a layi. Har an kwashe mun jerena har ga Allah ko ni a wancan lokacin na haƙura da Gwadabe. Allah ne yayi shan ruwan aurenmu bai ƙareba ina dawowa na samu wannan ciki." "Tashi daga tsugunnon Iyabo ki shiga ciki ke da Toye ki huta. Zan je in nemo miki abunda zaki iya ci, ko in sa Sakina ta yo miki" Da ƙyar na miƙe tsaye ƙafafuna sun yi tsami ainun. Haula da sauran matan dake wajen duk sai suka riƙe bakinsu akan furucin da Gwadabe yayi. Shi kuwa kamar ya faɗa ne dan ma ya sake cusa musu baƙin ciki. A'a Gwadabe kar ka nemo mini wani abuncin. Duk abunda na samu zanci, ai jikin nawa da sauƙi." Hannu nasa na sauke Toye daga kafaɗarshi. Ya miƙo mun jakar hannun Bara'u na rataya. Jakar kayanmu kuma nace ya tafi mana da'ita gidan Bara'u tunda acan yake sauka mafiya yawan lokuta. Ina tafe ina jan ƙafata. Sai kallon banza aketa watsomun, harda masu tsaki, da tofar da miyau. Duk inda naga taron mata sai na gaishesu zan wuce, kuma fa saina rusuna mu a al'adarmu akwai wannan tarbiyyar. Wasu su amsa ciki_ciki, wasu ba sa amsaba a haka har na isa ɗakin Babala. Cike dam ɗakin yake da ƙannenta da yayyenta. Yaya Halima ma ta dawo daga Rakiya tana zaune tana cin tuwon shinkafa miyar kabewa sai ƙamshin man shanu take yi. Laila na zaune a kusa da'ita ta ci ado sosai, sai wani hararata take yi. Ina shiga na zube a ƙasa ɗaya bayan ɗaya na dinga binsu da gaisuwa, har Laila dana girma ban bari ba sai da na gaisheta. "Sai ki tashi maza ki shiga cikin surukan gidannan ki kama aiki, baki ci ta zama ba" Cewar Baba Iyatu ƙanwar Babala. Miƙewa nayi ina shirin fita na jiyo Yaya Halima na cewa. "Ki tafi da ɗanki babu wanda zai kular miki dashi" Yaron na kalla yayi tsuru_tsuru kamar ba dangin mahaifinshi ya shigo ba. Duk ƙin Gwadabe da dangina suke yi bai shafi abunda muka haifaba sam, amman banda dangin Gwadabe. Hannun Toye na kama muka fito tare. Da Gwadabe naci karo zai shigo ni kuma zan fita. "Ina kuma zaki je ke da ba ishasshiyar lafiya gareki ba?" Ban ce mishi komai ba gudun kar in faɗi wata kalma da zata zama lefi. "Aiki zata je ta kama ma su Haula. Ko su zasu girka mata abinda zata ci ne rasa kunya?" Cewar Baba Iyatu. Da sauri na wuce shi ina murmushi wanda yafi kuka ciwo. Shi kuma ina jiyoshi yana musu bayanin hawan jini ne dani, kuma likita ya hanani yawan aiki da zurga_zurga. Ni dai gaba na ƙara dani akaita hada hadar girki har sai da muka gama na zauna a kan turmi ina ba Toye abinci a baki. Sakina ce ta iso inda nake da fara'arta. Nima cikin fara'a na tarbeta. Kwanon hannunta ta ajjiye a gabana. "Maman biyu ga farfesun kifi Gwadabe yasa nayi miki. Yace shi kaɗai kike iya ci ya zauna" Ɗan murmushi na ƙaƙaro na dubi Yaya Haula bata kallonmu amman kunnuwanta yana wajenmu. Kai Sakina sai da ya saki wahala? Kinga ga tuwo nan ma ina jira Toye ya ƙoshi ne sai in cinye ragowar, jikin yanzu da sauƙi" Da sauri Yaya Haula ta yi ɓangaren Babala na yi imani wata fitinar zata je ta kunno mun. Ɗakin Goggo Innawo mu ka shiga, ita Goggo Innawo ƙanwar mahaifiyar Sakina ce a gidan take aure. Anan naci kifina muna hirar yaushe gamo. "Oh Iyabo ashe rabon ƴan biyu ne ya dawo dake ɗakin ki. Irin rikicin da akaita tayi babu wanda ya zaci aurenku zai dawo, sai gashi har da cikin ƴan biyu" Dariya nayi nace. Sakina kinsan duk abinda ya samu bawa da sanin Allah. Shan ruwan aurenmu ne bai ƙare ba. Duk rikici in Allah ya riga ya ƙadarto a dakin Gwadabe zan ƙare rayuwata, babu tsumi babu dabara ga duk waɗanda basa son tarayyyarmu. Ni aurena da Gwadabe ya ƙara mun tsoron Allah, anan na sake gane ƙudurar Allah. Irin badaƙalar da ta biyo neman auren ai me girma ce, amman da yake Allah ya yarda da haɗin ba gamu ba". Sakina tace. "Wannan gaskiya ne. Mu kammu ba mui zaton aurenku zai yiwu ba. Duk da dai Gwadabe yana tsantsar sonki da burin son aurenki. Amman bai samu goyon baya a wajen kowa ba sai Bara'u. Bara'u kuma bashi da ikon zartar da hukunci a kan Gwadabe. Ba da ban Baba Magaji ba da yanzu wani labarin akeyi. Ke dai Iyabo ki ta yin haƙuri wata rana sai labari. Ko wacce mace da irin ƙalubalen da take fuskanta a gidan aurenta, muna barma cikinmu sirrinne kawai. Murmushi kawai nayi ina hango lokacin da Gwadabe yake zuwa taɗi ƙofar gidanmu a idanuna. Tun yana zuwa ana barinshi da dai Iyaa Debisi ta ga abun da gaske ne na riga na kamu da son Gwadabe sai aka hana shi zuwa gida wajena. Ni da Gwadabe sai dai mu haɗu a wajen da nake sana'ar tuyan ƙosai da kafa da daddare a bakin titin unguwarmu. Gwauron numfashi na ja kawai mu ka ci gaba da hirarmu da Sakina. Sai da na huta na yi sallar azahar. Muna yin la'asar kuwa aka aiko yaran gidan wai in zo bakin murhu za'a ɗaura sanwar dare. Faɗan irin wuyar da nasha ɓata lokacine kawai, aikin kusan nice ƙarfin yinshi, sukaita zamewa suna barina. Ga tuwon gidan bikin ƙauye ba tuwo bane na wasa, ni na talga tuwonnan na dinga ɗiba da ƙoƙo ina zubawa a tukunya lamba talatin sai juyawa ruwan zafin yake yi. Bayan na gama talge sai na koma wajen su Zuwaira mu ka ci gaba da wanke kwanukan da aka ɓata da rana. Wanke_wanke ne bana wasa ba. Muna tsaka da wanke_wanken Su Yaya Hambali suka zo wucewa ta wajen. Dukkansu suke tafe harda Gwadabe wanda na ga idandunanshi sun kaɗa sun yi jawur. Duk da magriba ta kawo kai akwai ƙarancin haske. Kallona kawai yayi ya girgiza kai suka wuce zuwa shiyyar Babala. Haka kawai sai na tsinci kaina a cikin damuwa gami da faɗuwan gaba, take sai jikina ya mace murus. Cikin dauriya na iya tsaiwa muka kammala duk aikin daya kamata Gwadabe:. Tunda ya shiga ɗakin Babala, Babala ta tare shi da ruwan faɗa itace harda kukan ta ji labarin Iyabo ta shanye shi, ta mai sheshi Ɗan aikinta. Duk ta hanyar da yaso ya ɓullo mata dan ta fahimci dalilin da yasa yake mata aiki, amman Babala ta fututtuke. Su Goggo Iyatu suma suka ara suka yafa, mai makon su rarrashi ƴar uwarsu sai ma sake zugata da su kai ta yi. "Wallahi Kyauta wannan lefinki ne. Dan wallahi da nine Tanimu ya kwaso mun ƙabila da sunan matar dazai aura. In sama da ƙasannan zata haɗe bazai aureta ba. Ki duba yanda ya shure soyayyar ƙanwarsa Laila fa Kyauta. Da ba dan na kai zuchiyata nesa ba da zumuncinmu ai ya taɓu" ( Kyauta sunan da dangi ke kiran Babala dashi kenan. Babala kuma sunan da ƴaƴa da jikoki ke kiranta kenan) Cewar Goggo Iyatu kenan. Goggo Jummalo tace. "Ai yanzu ma bata ɓaci ba Iyatu. Har yanzu Gwadabe zai iya auren Laila. Tunda har Laila ta iya kaso aurenta domin tana son Gwadabe .Ya kamata a wannan karon ya aureta ko dan dole dan ubanshi a nuna mishi mu muka haifeshi ba shi ya haifemu ba. Wallahi a wannan karon aurenshi da Laila babu wata makawa." Da sauri Gwadabe ya ɗago jin labarin mutuwar auren Laila ba ƙaramin kiɗimashi lamarin yayi ba. Ga wata magana da Goggo Jammalo take faɗe, shi yanzu ina ya ga ta yin aure alhalin abinci ma da ƙyar yake iya kaiwa gidanshi, har yanzu bai soma sana'a a matsyin ogan kanshi ba. Ta yaya ma zai auri Laila? Wannan ma maganace da bata dace ace an ma tare shi da'itaba, duba da irin halin talaucin da yake ciki, da kuma babban dalilinshi na ƙin Lailan a bayan. Da ƙyar Gwadabe ya yakice ya bar ɗakin Babala yana yarfe zufarshi. Yana hanzarin barin shiyyar ya jiyo muryar Laila a bayanshi tana kiranshi. "Gwadabe ji mana dan Allah " Cak ya tsaya bai juyo ba, bai da niyyar juyowar. Sai itace ta tako har inda yake, ta fuskanceshi. "Gwadabe guduna kake yi ne?" Kallonta Gwadabe yayi, tare da girgiza kan shi. "Tayaya zan guje ki kina gudan jinina Laila? Na ga ai mun gaisa ko, ko akwai wani abunne bayan wannan?" Ɗan murmushi Laila ta yi tare da cewa. "Babu komai. Ka ji labarin mutuwar aurena, da musabbabin mutuwar tashi ko?" "Ai kina jiyo duk bayanin da su Babala suke yi mun. Allah ya daidaita tsakaninku da mijinki. Laila in da gaske dan ni kika fito daga ɗakin ki, kin tabka babban kuskuren da zaki jima kina cizon yatsan ki. Sam ni Gwadabe bani da ra'ayin ƙarin aure, lafiya lau muke zaune da Iyabo, bata rage ni da komai ba, ta bani dukkan lokacinta da zuchiyarta. Haka zalika ni ma zuchiyata tana gareta. Ina mai baki haƙuri a karo na biyu." Yana dasa aya ya wuce ya barta da jin kunya. Yana tafe yana mamakin irin ƙiyayyar da su Babala suke yi ma Iyabo, duk da dai shima irin wannan tsanar akayi mishi a gidansu Iyabo. Da dama a cikin gidansu Iyabo basa ko amsa sallamarshi. Bayan sallar la'asar kuma Babala tasa akayo mata kiran kab yaran nata, dan Haula ta tsokata mata abinda ya faru a can gida Kano da safe kafin su tawo. Shine wannan wucewa da Iyabo taga sunyi. Bayan sun gurfana a gaban Babala da Goggo Iyatu, da Goggo Jammalo, da Goggo Takura. Duk waɗannan ƙannen Babala ne, babban wansu Baba Magaji shi yana Maraɗi tare da iyalinshi. Nan Yaya Hambali ya soma yi ma Babala bayanin abinda ya faru, harda ma waɗanda suka wuce. "Babala Iyabo ta gama mallake Gwadabe, shi yake yi mata komai da kika sani. Wallahi Babala har ruwan wanka sai Gwadabe ya kai mata, haka zaki ga ta fito tana kallon su Haula ɗaɗɗaya. Duk abunda Gwadabe ya samu akanta yake ƙarewa tas. Ai kin ganta sai ƙiba take narkawa, shi kuma yana ƙarewa kamar wanda ake lasa. Ni shi yasa nace su bar mun gidana kawai, dan ba ƙaunar buɗe idanu nake in ganta a cikin gidan ba Babala. Tunda har Gwadabe ya soma takamun burki, wataran sai duka. Kafin akai ga hakan gara su tashi kawai, ina da buƙatar wajen nasu dama zan zuba dabino a ciki. Babala irin taɓarar da Gwadabe da matarshi suke yi a cikin gida kare fa bazaici ba. Wallahi sai ki ganshi da gajeren wando yana barbaɗa mata garin Amala ita tana tuƙawa sunayi suna waƙar yarbawa. Wannan baƙin ciki da mi yayi kama" Yaya Harisu yace. "Gaskiya ne gara ya kama mata haya a can nesa damu Babala. Ƙazantar da baka gani ba tsabta ce. Dan wannan yaron baya ko jin kunyar idanunmu, wallahi zaki ganshi a tsakar gida yana wanki tana mishi shanya, wataran har waƙar yarbawa zaki ji suna rerawa abun takaicin ya iya waƙar. Gwadabe ya rasa wacce yake so duk dangi, duk cikin ƙabilunmu na Hausa fulani kyawawa, sai wannan buskutar beyerabiyar ce ta ja hankalinshi." Haka ɗaya bayan ɗaya kowa ya goyi bayan Gwadabe ya bar ma Yaya Hambali gidanshi. Shi kuwa gogan yayi ƙuri yana jiran irin hukuncin da Babala zata yanke. Gyaran murya tayi tare da cewa. "Na ji bayananku kab, kafin ku koma za ku ji hukuncin dana yanke. Zanyi shawara da ƴan uwana, akan batun matarshi kuwa wannan ƙabilar? Alkadarinta ya riga ya kusan karyewa. Ku tashi kuje in Allah ya kaimu gobe zaku ji hukuncin dana yanke" A sanyaye Gwadabe ya bi bayan ƴan uwanshi. Zuchiyarshi cike da ƙuna gami da taraddadin me ka je ka zo. Iyabo: . Sai zuwa bayan isha na samu hutu. Duk mun baje a tsakar gida muna shan iska. Ina kwance akan tabarma nayi matashin kai da hannuna. Toye yana zaune a gabana. Ƴan uwa sai hira da shewa suke ta ta yi abun gwanin ban ƙawa, ni kuwa mujiya na kasance a cikinsu, komai a tsorace nake yinshi, bana son in ɓata ma dai_dai da yaron gidan na goye rai. Ina gani ɗazu yarinyar Asiya matar Lawal tana dukan Toye, babu wanda ya kula. Gashi ba sa'arshi bace dan zata yi shekaru tara da doriya ma. Sai da ta gaji dan kanta ta barshi. Ina kwance barci ya soma dibata Yaya Halima ta zo inda nake tai mun ƙerere a ka. "Mandiya hamshaƙiya sai ki taso ga can kayan miya da su alayyawo zaku gyara, gobe da asuba za'a aza tukunya" Da sauri na miƙe ina faɗin wash dan wani irin ƙara ƙuguna yayi mun mai zafin gaske. Toye na kwantar ya riga ya soma bacci a zaune. Tunda muka zauna zaman aikinnan ba mu bar aikin ba sai wajajen sha biyun dare, sannan kowa ya kwanta. Da asussuba kuwa washe gari muka tashi da aikin tuwo, dan kafin takwas na safiya mun kammala tuwonnan tas mun malmalashi mun jera a fantekoki. Zuwa ƙarfe sha ɗayan rana gidan biki ya cika danƙam da jama'ar biki, sai haya_haya kawai kake ji. Daga waje ma haka ƙofar gidan take danƙam da maza ƴan ɗaurin aure. Yaron Sakina ne yazo ya kirani. "Umman Toye wai inji ummata kizo ki yi wanka" Allah sarki ni Iyabo. Kowa a gidan sai wanka akeyi ana kwalliya, yara da manya. Amman ni babu wanda yai mun ta yin wanka. Bin bayan yaron nayi har zuwa gidansu. A falon Sakina na samu Gwadabe da Bara'u suna zaune suna cin tuwon biki. Ƙur ya ƙura mun idanu, take na ji hawaye na shirin zubo mun, har numfashina na karkatsewa. Fitowar Sakina daga uwar ɗakine ya katse kallon ƙudan da muke ma juna. "Maman biyu tun ɗazu nake ta jiranki ki zo ki karya ku yi wanka ke da Toye, sai mu ka ji shiru kuma" Kujera na samu na zauna duk illahirin jikina babu inda baya yi mini ciwo, kuma babu inda bai yi mun tsami ba, zazzaɓi ne kau a jikin nawa ma, ga jiri da ke damuna. Ke dai bari, aikin abincin bikine bai bani damar zuwan ba. Kinga ko karyawa ma ban yi ba. Bara'u ina kwana ya akaji da taro?" Na faɗa kaina a ƙasa. "Lafiya lau Iyaa Toye Tsuntsun soyayya, ya jiki_ jikin?" Alhamdulillah. Na dubi Gwadabe nace. Ekaro oromi ( ina kwana mai gida?) Ajjiyar zuchiya ya sauke kana yace. "Kin tashi lafiya, ya jiki_jikin naki? Wato kina ta aiki bayan kinsan likita ya hanaki aiki mai wuya ko? Gobe ma kowa zai watse daga yau biki ya ƙare, tunda yau za'a kai Amarya ɗakinta ai" Boyayyar ajjiyar zuchiya na sauke, dan jina nake tamkar a ƙaya wallahi. Zame jiki Bara'u da Sakina su ka yi su ka bar mana ɗakin. Suna fita Gwadabe ya dawo kusa dani ya zauna. "Iyabona" Ya faɗa muryarshi na rawa. Kuka na fashe mishi dashi. Gwadabe na roƙeka da girman Allah ka sauwaƙe mun zuwa taron biki ko suna na danginka. Ba ƙaramin muzanta nake yi ba. Ka ware mana wasu lokutan domin ziyarar danginka, amman ba lokacin wani sha'ani ba." Shiru yayi yana kallona idanunshi suka kaɗa su kai jawur. "Ki ƙara haƙuri bisa wanda kike yi da dangina Iyabo. Nasan kina takura sosai, kuma kina shan baƙaƙen maganganu marasa daɗin saurare. Amman ni ko na so barinki a Kano, kinsan ba yarda Babala zata yi ba. Kuma hakan zai ƙara haddasa wata fitinarne. Iyabo bana son kukan ki, ki share hawayenki gobe da wuri zamu bar Takai ki yi haquri kinji?" Sai na ji tausayinshi ya kuma kamani, ga ɓoyayyar damuwa ina gani shinfiɗe a fuskantar shi, duk da yana ta ƙoƙarin ganin ya ɓoye mun halin da yake ciki. Amman na san Tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi. A hankali na furta. Gwadabe na ganka a cikin damuwa meke damunka, kar kayi yinƙurin ɓoye mun, dan bama ɓoye ma juna damuwarmu. A kai nane ko Gwadabe?" Ajjiyar zuchiya ya sauke, tare da kamo hannayena dukka biyun ya ɗan matsesu kaɗan. Idanu na lumshe ina cike da tsantsar tausayin aurenmu. MRS BUKHARI *DAN ALLAH KUIMUN AFUWA NA SAURARI ƘORAFE_ƘORAFENKU AKAN KU WATA BIYU YAYI MUKU YAWA. AYIMUN AFUWA MU BARSHI A WATA BIYU, NA SAKE TURO WANNAN PEJINNE DOMIN IN MUKA DANNAR ƘIRKI DASHI. NAN DA WATA BIYU ZAKU JINI DA CI GABAN LABARIN NAGODE*🙏🏻🙏🏻 https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU. ROMO ƊANYE BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Lamba ta uku "A game da abinda ya faru a gida can Kano ne kafin mu tawo. To da Yaya Hambali, da su Yaya Harisu duk sun amince akan Yaya Hambali ya tashe mu a gidanshi mu yi nesa dashi. To Babala tace dai a barta tayi shawara da su Goggo Iyatu. To kinsan Goggo Iyatu kusan ita take sake zuga Babala akan ki. Sabida Laila ƴar wajenta da Allah bai yi mun yi aure ba kamar yanda suka tsara tun muna tsumman goyo. To kinji abinda ya ɗaga hankalina kenan, tunda nasan bani da kuɗin da zan iya kama mana ko ɗaki ɗaya, balle ciki da falo." Ƙur na zuba mishi idanu. Gwadabe duk abinda Allah yayi a kan mu me kyau ne. Allah ba zai ba danginka ikon tozarta mu ba da ikon Allah. Kayi haƙuri jarumina duk a akaina ake yi ma hakan." Murmushi yayi gwanin tausayi yace. "A tunaninsu matsa mun lamba da zasu ci gaba da yi, shi zai sa aurenki ya sire mun. Billa aurenki kullum sake zame mun yake yi kamar yau aka ɗaura iyabo na. Kema ki ƙara haƙuri wata rana sai labari . Sannan ina da babban albishirin da na cancanci garjejen farin goro ɗan shagamu. Allah ya nufa nima na zama matuƙin Babbar mota na tashi daga karen mota. Ma'ana an mallakamun mota." Sakina ce ta shigo hannunta riƙe da langa da kofin silver ta dure shi a gabana. "Sakko ki ci abinci ki yi wanka mu samu mu koma gidan biki, yau biki zai ƙare Amarya zata kwana a ɗakinta" Godiya na yi ma Sakina. "Gwadabe Bara'u yana ƙwar gida wai kaje ku tafi" Da sauri ya miƙe, mu kai sallama ya fice dan yanzu za'a ɗaura auren ƴar autar tasu. Ni ko a gurguje na karya na yi wanka zuchiyata fal murna na san a ƙalla zamu samu sassauci daga talaucin dake addabarmu. , Sakina ta yi ma Toye wanka. Leshin ankon bikin Bose da mu ka yi wata shida daya wuce na saka. Leshi ne me tsada, dan ko sanda aka fitar da leshin na cire raina da yi, amman Gwadabe sai da ya je ya ciyo bashi yai mun domin ya fitar dani kunyar dangina, leshin ya sha ɗinkin buba da zani, na saka sarƙa fashion me kyau wacce Gwadabe ya siya mun a legas da suka je. Mayafina da takalmina ma sababbine wanda matar Tamu ta aiko mun daga Habuja, da naso in bari sai na haihu in yi fitar suna dashi. Gwadabe ne ya ƙi yarda yace lallai sai dai in sa a bikin gidansu nima in fito da kyau, dan su Yaya Haula suma sun yi ɗinke_ɗinken biki kala uku_uku. Ni kuma bamu da kuɗi leshin da na sa basu san na ɗinka ba, tunda mu ka yi bikin na ɓiyeshi a ƙasan akwati abunka da tattali irin na talaka. Fitowa nayi shar dani har ƴar hoda da jan baki na murza. Toye kuma riga da wandon Atampa na saka mishi da hular ashoke irin na yarenmu. Sakina ta riƙe mishi hannu muka nufi gidan bikin. Ƙofar gidan taƙi wutuwa sabida tsabaragen dandazon maza ƴan ɗaurin Aure, sai maƙota muka faɗa akan in an sassauta ma shiga cikin gidan. Sai wajajen kusan azahar ƙofar gidan ya sarara da mutane muka samu muka shiga cikin gidan. Da Laila na soma haɗa idanu, sai naga ta shiga ƙarame kayan jikina kallo har kirjinta na hawa da sauka irin na tashin hankali. Ni mamakine ma ya kamani. Ban bi ta kanta ba kai tsaye shiyyar Babala na wuce domin in sake gaishesu. Kowa na cikin ɗakin kallona yake yi baki a sake, Yaya Haula kuwa tsabar kallona da ta shagala tana yi sai da ta zuba ruwan miya a ƙafarta mai zafi kafin ta dawo hayyacinta. Koddibuwace babba a jikinta, amman leshina ya tsole mata idanu. Yaya Halima kuwa wuyana take ta kallo kawai. A tsarge na gaggsishesu bi da bi, suka amsa a daddaƙile in da sabo na riga dana saba tuni. Na ɗan zauna jim sai ga Amarya ta shigo ɗakin ita da ƙawayenta su su biyu. Ta tsugunna ta gaisa da kowa amman kallo wannan ban isheta ba. Sauwama Amarya an sha kyau" na ce mata ina ɗan yaƙe. In kun tanka yarinyarnan ta tanka. Abunda ya kawota ta yi ta fice da ƙawayenta. Bayan na zauna kamar na awa ɗaya haka sai na koma tsakar gida, dan naga atana alwalar sallar azahar. Ɗakin ƙanwar mahaifiyar Sakina anan nayi Sallah, mu ka ci tuwo da Sakina, na koma tsakar gida muka shiga rabon tuwo ka'in da na'in. Ban zauna ba sai da aka gama rabon abinci kab tukunna. Zuwa bayan laa'asar kuma dangin ango suka tawo da fantimotin aure, daga nan kuma zasu tafi da Amarya. Ayarin su Asiya na bi mu kai ta fita da kayan ɗakin Amarya ana sakawa a mota. Su Yaya Haula da Zuwaira harda su a ƴan kai Amarya, mutane sai da suka cika Bus guda, sai ƙaramar motar Amarya da ƴan ƙawayenta. Muna shiga cikin gida muka tsaida sanwar tuwon dare ba mu muka nitsa ba sai wajen takwas na dare, sai lokacin na samu kaina na galabaita sosai, marata ciwo take yi mun tun rana haka na kwana da ciwon marar nan. Da sassafe muka kuma tashi da aikin gyaran gida da karin kumallo. Kokko da ƙosai mu ka yi, bayan an kammala karyawa baƙi suka shiga haramar komawa garinsu, sai wanka akeyi. Sai da mu ka yi wanke_wanke muka share wajen tas kafin na samu bokiti na samu ruwan wanka mu ka yi ni da Toye. Gwadabe ne ya neme ni a tsakar gida ya same ni. "Ki hanzarta ki shirya yanzu zamu kama hanyar Kano. Ana mun lodi a mota zamu kai kayan Legas." Ajjiyar zuchiya na sauke nace. A shirye nake ni kam tsab. "To ki shiga ki yi sallama da matan gidan, sai ki same ni a ɗakin Babala" Yana faɗar haka ya juya da sauri. Ni kuma na shiga bin ɗakuna inai musu sallamar zamu koma, har na iso ɗakin Babala na shiga da sallama. Su Yaya Hambali duk suna ɗakin, waje guda na samu na raɓe. Babala dake magana taci gaba da magana. " Kai wannan yaron ka yi haƙuri ka bar Gwadabe ya zauna a tare da ku. Dan ina buƙatar a dinga sa mun idanu akan dukkan motsinshi. Amman ya dinga biyanka haya a shekara, in yaso sai ka kama shago da kuɗin ka dinga tara dabinon naka a ciki. Kai kuma Gwadabe duk shekara ka dinga bashi nera dubu ashirin kuɗin hayar ɗakinshi. Dan in ma baka bashin ba akan matarka zai ƙare. Gara ka ba ɗan uwanka dan babu irin hidimar da bai ma rayuwarka ba. Shi ya cicciɓaka har ka kai wannan matsayin. Ke kuma Iyabo zan gargaɗeki duk randa kika sake yi musu gwale a tsakar gida, ni na basu umarnin su watso miki da kayanki waje. In shi kin shanyeshi sai abunda kike so yake yi, to ni na sha tabara na sha yaseen ke har da lahaula duk na haɗa na sha na fi ƙarfin Oremi ma uwar bokayen yarbawa balle ke karan kaɗa miya. Ni dai kaina na ƙasa numfashi mai ƙarfi na saka fesarwa, in tashi in fita ina jin tsoron fassarar da zasu yi mun, in ci gaba da zama zuchiyata ta buga, hawaye na soma zubarwa. Yaya Hambali da su Harisu ransu yai fari fes dan jin irin hukuncin da Babala ta yanke mana. "To Shikenan Babala dan kin sa baki ne zan barsu su biya haya, amman da ko hayar basu isa na basu ba, dan dubu ishirin ɗaki ɗaya zai iya kama musu. Babala ki faɗa mishi na bashi sati ɗaya ya biya kuɗin haya, dan haya zata soma daga yau. Ban yarda kuma a sake sa mun kaset ɗin yarbawa a gidana ba." Ni sabida tsabar mamaki daskarewa nayi a zaune ina jin ikon Allah. Gwadabe kuwa kasaƙe yayi in wannan yayi magana sai ya juya ya kalleshi, har sai da suka gama maganar tsab yace. "To na ji Babala zan dinga biyan kuɗin hayan kamar yanda kika gindaya mun in sha Allah. Yaya Hambali kayi haƙuri a bisa dakatar da kai da na yi. Kuma in sha Allah in akwai wata doka ma da kakeson gindaya mana, zamu yi ƙoƙarin ganin mun bi, ai kai ubane ba wa a gareni ba. Babala shikenan inason mu tafi ana ma motarmu lodi legas zan wuce a yau ɗinnan?" Babala ta yi murmushi tace. "Me kake ci na baka na zuba, yanzu zan sallameku ai." Baki ta kada ta kira Laila har sau biyu kafin ta amsa daga uwar ɗakin Babala. Fitowa tayi tana wata irin tafiya ta jan hankali. Kallonta nayi inason in karanci yanayinta, ita kuma idanuwanta akan Gwadabe suke. "Kin gama haɗe kayan tafiyar naki dai ince?" Babala ta tambayeta, sai da ta yi murmushi har da sin da kai kafin tace. "Na gama haɗawa tun jiya Babala" "To ki fito da fantimotanki zaku wuce yanzu ko?" Laila ta kalleni muka haɗa idanu kafin ta koma uwar ɗakin. Babala kuma tace da Gwadabe. "Ga Laila zaka tafi da ita ta zauna a hannunka. In kun daidaita kanku falillahil hamdu, mu haka muke so dama. Kai na ɗauki amanar Laila na ba, sai ka kula da'ita yanda ya kamata. Ka kuma tuna ƴar uwarka ce, gyatumarta ni na saki nono na bata" Ba ƙaramin razana nayi da jin wannan zance mai kamar saukar aradu ba. Meke shirin faruwa dani ni Iyabo a wannan karon? Ta ya za'a bamu riƙon gansamemiyar bazawara irin Laila. Lailan da ada mijina ita zai aura, kuma har yanzu data fito naga son Gwadabe a idandunanta. Tabbas an shirya hakanne dan a nuna mun iyakata, ai mun kora da hali. In zan iya ɗaukar duk irin samfurin wulaƙancin da dangin Gwadabe suke yi mun, bazan iya jurar wannan ba, tabbas sai dai Laila ta mayema Gwadabe gurbina dan tafiyata zanyi gidanmu, abun ya isheni haka" "Babala taya zan iya riƙon Laila ina ƙarami alhalin ga Yaya Hambali, ga Yaya Harisu, sannan ga Sukairaju. A tunanina su yafi cancanta su rike Laila tunda sune a gaba dani. Sannan Babala..." "Ya isheka nace. Na riga da na yanke hukunci kai baka isa ka koya mun yanda zan yi ba. Ka tashi kawai ku wuce in ba so kake ranka yai mummunan ɓaci ba" Cikin faɗa sosai Babala take yin magana, har muryarta tana rawa. Ba shiri na miƙe har wani jiri nake gani tsabaragen kishi. To Babala zamu koma, sai mun sake zuwa kuma. Amarya Allah ya zaunar da'ita lafiya a gidanta" A mugun fusace Babala tace. "Ameen in da gaske kike yi baƙar muguwa kin rabani da abunda na haifa. Kema in sha Allah haka wata zata rabaki da ɗanki kiji in da daɗi" Bance uffan ba na ja hannun Toye muka fita bana ko gani da kyau. Ji nayi duniyar na juyawa dani, kaina na wani irin saramun tamkar zai rabe biyu. A ƙofar gida na nemi dakali na zauna jikina na rawa. Tsawon shekaru shida ina shanye dukkan abunda dangin Gwadabe suke yi mun. Amman ji nake yi kamar ma zamana da Gwadabe ƙarshe yazo kawai. Wallahi bazan iya dai dai da kwana ɗaya a ɗaki tare da Laila ba. Gara ni in matsa sai su aura mishi ita zaifi. Wasu zafafan hawayene suka gangaro a kumatuna. Ƴar ƙaramar wayata ce ta soma kuka, wayar da tunda nazo ba wanda ya kirani sai yanzu. In zaro wayar a jakar na kasa sabida tsabar turirin da zuchiyata take yi. Laila ce ta fita kici_kici da fantimotai guda uku hawan hawa, harda wata ƙatuwar jaka. Sai fara'a take yi tamkar wacce akaima bushara da gidan aljanna. Kawar da kaina nayi dan bana ƙaunar sake ganin fuskar Laila. A sanyaye Gwadabe ya fito daga cikin gidan. Duk yanda yaso mu haɗa idanu naƙi bashi damar hakan. Bara'u da Sakina ne suka katse mana tunaninmu. Gwadabe ya janye Bara'u zuwa gefe. Sakina ta zauna a kusa dani hannunta riƙe da baƙar leda. Laila tana daga gefe tana amsa kiran waya. "Meke faruwa Iyabo duk na ganku a birkice haka, naga Laila da fantimotan aurenta?." Hmm Babala ce ta danƙa amanarta a hannun Gwadabe, suna nufin tare da kishiyata zan zauna, bayan ta gama sanin sirrina sai a bashi umarnin aurenta." A hasale nayi maganar kuka na tunkuɗo kanshi. Sakina ta riƙe haɓarta tare da sakin baki cike da ta'ajibi tace. "Danƙari maƙari. Kika ce me, Lailan ce zaku tafi da'ita ta zauna a wajenku? Lailan da duk ƙauyannan ba wanda baisan irin son da take ma Gwadabe ba. Ke a wata ruwayar fa cewa akayi sabida Gwadabe ta kaso aurenta. Haka naji a wajen Goggona, kuma hakanne Bara'u ma ya sani. " Kaina ne naji yayi wata iriyar buɗewa, gabana yaci gaba da harbawa. Zuchiyata ta shiga watsa jini bisa rashin ƙa'ida, take na soma haki tamkar numfashina zai dakata. Yawu nake so in haɗiya in jiƙa maƙoshina da nake jin tsabar bushewa ya shiga daddarewa. Kika ce me Sakina?" Da ƙyar na jawo numfashi daga huhuna zuwa cikin bakina, harshena kuwa da ƙyar na iya sarrafashi. "Wallahi Allah kinji na rantse Laila sabida Gwadabe ta kaso aurenta, kowa ya sani." To gata ga Gwadaben, dan ni muna isa zan tattare inawa inawa in bar musu filin ɗakin, tunda dama abinda suke so kenan. Wallahi Sakina bazan iya zama inuwa ɗaya da Laila ba, gidanmu zan koma" Hawayena yaci gaba da zuba a kan kumatuna. Dafa kafaɗata Sakina tayi tace. "Bazan ce kar ki ƙwaci ƴancinki ba Iyabo. Haƙiƙa kin shanye abubbuwa masu yawan gaske tun daga aurenku kawo iyanzu. Amman barma Laila gidanki ba mafita bane Iyabo. Kiyi tunani kafin yanke hukunci, kar ki aikata aikin da zai jefa ki cikin dana sani marar amfani." Murmusawa kawai nayi dan banji akwai abinda Sakina zata faɗa yai tasirin hanani barma Laila Gwadabe ba." Gwadabe Yana fitowa ya dubi inda Iyabo ta zauna, zamanta kawai ya duba yasan tana cikin damuwa mai yawan gaske. Amman da zata tona taga irin damuwar da yake ciki zata san damuwarshi ta dame damuwar da take ciki ta shanye. Ya jima akan Iyabo yana son su haɗa idanu domin karantar yanayinta amman fur taƙi yarda ta ɗago. Dama muddin Iyabo na cikin ɓacin rai bata yarda ta ɗago kanta, sannan bata iya furta kalma. Isowar su Bara'u ce ta dawo dashi hayyacinshi. Gefe guda abokin nashi ya jashi. "Wadannan fantimotan ba na Laila bane Gwadabe. Kano zaku tafi da'ita ko me? Kasan zamanta gida ɗaya da matarka ba zai haifar da ɗa mai ido ba ko? Iyabo fa tasan irin soyayyar da Laila take yi ma, a lokacin da take ƙarƙashin inuwar auren waninka ma, ta kasa barin zuchiyar Iyabo ta nutsa, balle yanzu da nayi imanin farautar zuchiyarka zata je yi. Gwadabe ya kamata su Babala da Goggo Iyatu su ƙyale Iyabo ta nutsu, ta sha ruwa a gidanka. Yarinyace mai hankali da biyayya, gata da tausayinka, son da take yi ma mai tsananine. Shin ko dan so da ƙaunar da take yi ma ba hujja bane da zai sa Babala ta haƙura ta barku kuyi rayuwar Aminci ba?" Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke yace. "Ni bansan da wanne idan ma zan kalli Iyabo ba. Kar kaso kaji irin cin fuskar da Babala ta gama yi mata yanzu. Ba wanna ba Bara'u kasan ni Babala ta ba riƙon Laila a ɗakina zata zauna? Bayan hakan har tana ƙarawa da faɗin in mun daidaita kammu su hakan suke so. Ina cikin tsaka mai wuyar fita, ina jin nauyin Iyabo sosai, tana haƙuri da yawa da dangina." Bara'u ya dafe ƙirji tamkar wata mace yace. "Gwadabe kace Babala ce da kanta ta baka riƙon Laila, alhalin tasan ɗakinka ciki da falone kuma ƙananu, a haka take so ku zauna da Lailan duk abinda kuke yi tana jiyowa? Zaman ma bazai yi kyau bane Gwadabe kuma in akace an yi hakan to tabbas an zalinci Iyabo kuma an shiga hakkinta. Tana da damar yi maka bore ko tawaye. Kuma itama Babala dole ayi mata biyayya a matsayinta na uwa. Amman Gwadabe kar in tsayar daku kuje. Ni kuma zan shiga in samu Babala mu tattauna wala Allah zata fahimcemu. In yaso Laila ta zauna a wajen Haula tunda ita babbace kuma tana da ɗakin ƴan matan yaranta. Duk da hakan zaman ba kyau zai yi ba, amman in muka samu hakanma dama_dama. Dan Allah ka ba iyabo haƙuri ni wallahi kunyarta nake ji ma" Kai Gwadabe ya ƙyaɗa yace. "Kar ka wahalshar da kan ka da yawun bakin ka Bara'u. Ni nasan ko sama da ƙasa haɗewa zata yi, Babala ba zata saurareka ba balle ta fahimceka. Ko kasan yanzu haya zan dinga ba Yaya Hambali har nera dubu ashirin a shekara, ina nake da irin wannan kuɗin Bara'u?" Jijjiga kai Bara'u yayi yace. "Maganar tana da tsayi, da girma Gwadabe. Ungo Bakonnan shinkaface, da masara, sai kuka da daddawa, da gyaɗa da Sakina ta saka muku, ku kama hanya. Zanzo da zaran ka dawo daga legas, sai mu tattauna. Ta yi haƙuri ita Iyabo kafin mu tsayar da mafita. Muje suna jiranmu" Iyabo:. Ni dai ina zaune kamar mutum mutumi . Ita kuma Sakina sai gargaɗi take yi mun akan duk rintsi kar in kuskura in bar Laila taci nasara a kaina, kana kar in kuskura tasan logona na zafin kishi dan zata wahalani dashi. Jinta kawai nake yi, dan banga abinda zaisa in zauna inuwa ɗaya da Laila mu gauraya numfashi a ɗaki tare ba. Duk wannan abinda akeyi Laila na tsaye a gefe da Samarin cikin gidansu Gwadabe tana hira, duk da nayi imanin hankalinta na garemu. Su Bara'u ne suka nufo mu. "Tsuntsun soyayya to shikenan Allah ya tsare hanya. Aita haƙuri duk abinda yai farko ƙarshenshi yana tafe ko mu jima, ko mu daɗe. Allah ya yi miki albarka bisa bin mijinki da kike yi mun gode, in Allah ya saukeki lafiya Sakina zata zo da wuri ayi komai da'ita. Kuma a miƙa mun saƙon gaisuwa zuwa ga Iya Debisi, da Debisin" Ameen nagode sosai." Iyakar abunda nace kenan dan muryata shaƙewa tayi." Mashin Sakina ta tarar mun na hau, ta ɗaura mun fantimotina a gaba, ta miƙo mun ledar hannunta. "Amshi Atampa ce, kya ɗinka ki ƙara a kayan cin suna" Kafin in mata godiya har ta shige gidansu Gwadabe. Gwadabe ya hau mashin shi da Toye, da jakar kayanshi. Itama Laila ta hau nata aka ɗaɗɗaura mata kayanta muka wuce. Ina zaune akan acaɓa tunani duk ya addabeni, na rasa inda zan tsoma kaina. In na bar gidan Gwadabe na tafi gidanmu, bani da tabbacin Iya Debisi zata amsheni, kuma ko bata amsheni ba, sai ta yi mun kwakwazo da tonon sililin da kab ƴan gida sai sun sam halin da nake ciki. Ƙauyan da mahaifiyata take Aure kuma sau ɗaya na taɓa zuwa, shima a lokacin ina da shekara goma sha biyu ne. In wuƙa za'a ɗaura mun bisa wuya ko sunan ƙauyan bazan iya tunowa ba. Kuma har ga Allah bazan iya zama da Laila a ɗakina ba. Ajjiyar zuchiya na sauke wanda yayi dai_dai da isowarmu inda zamu hau mota. "Cikin gari ne, Alhaji, Hajiya kuzo ga mota" Cewar ma'aikatan tashar, suka yo kanmu suna rige_rigen sauke mana kayanmu zuwa wata cinyayyar Bus wacce ta ga duniya. Ni dai ina biye da mijina. Waje ya sama mun na zauna, Laila kuma ta zauna a jerin kujerun farko. Sai ajjiyar zuchiya nake faman yi. Ina hango Gwadabe ta taga yana biyan kuɗin motarmu, bayan ya biya ya shigo cikin motar. "Ga waje na samama kamar zaifi cikin sanyi ko?" Cewar Laila, tana yi tana kashe muryarta kamar tsohuwar karuwa. Tsaki ya ja bai ce mata uffan ba ya wuto inda nake a baya, yana riƙe da Toye. Zama yayi a kusa dani baice mun komai ba, amman naji jikinshi yayi zafi kau halamun zazzaɓi. Idanu na lumshe hawaye suka zubo mun suka diga a tsintsiyar hannunshi, kasancewar a mugun matse muke a motar. Ɗagowa yayi ya kalleni, ni ko kaina na kallon waje. "Iyabo so kike ki ƙarasa sukurkutamun lissafi kenan, ni da zan kwana a hanya ina tuƙi. Shin in ban samu sassauci a wajenki ba ina zan shiga in ji daɗi? Dubi yanda kike asarar hawayenki ke da baki da ishasshiyar lafiya" Da raɗa_raɗa yai mun maganganun. Zuchiyata ta tsinke, sai naji sababbin hawaye suna gudu a kumatuna. Allah ya gani bazan iya zama da Laila ba zaman da bansan irin sharrin da aka tanadar mishi ba tunda abun shiryayyene. Hawayena na share dan in sama ma Gwadabe ƴar nutsuwa. Amman sai na kulle idona kawai kamar mai bacci. Har motarmu ta fice a tasha, ta ɗauki hanya ban buɗe idandunana ba, banda niyyar buɗewa. Amman idanuna biyu zuchiyata na faman yi mun turiri. Ina jiyo muryar Toye yanai ma Gwadabe yarbanci, yana bashi amsa da yarbancin. Duk da ba iyawa yayi sosai ba, amman yana ƙoƙari wajen koyo, dan lokaci mu ka saka na musamman a tsakankanin magriba ruwa isha, ina koya mai yana maimaitawa in ya haddace sai ya rubuta. Wasu kalmomin da ƙyar yake iya furtasu. Muna nishaɗi sosai dan dariya muke yi sosai har tsakar gida ba za'a rasa jiyomu ba. A tsakanina da Gwadabe rayuwa muke yi mai aminci, muna ƙoƙarin bama junanmu farin ciki, da bama juna cikakken lokacin juna. Wannan irin zaman ke ƙaramun so da tausayin Gwadabe a ko wanne daƙiƙa. Shima hakan ke ƙara mishi sona. Bama iya ɓoye ma juna dukkan wani sirri. Haka naita tunane_tunanen daddaɗan zaman da muke gudanarwa da Gwadabe na. Zamanne danginshi basa so, sabida na fito a ƙabilar da ba tasu ba." Nasha wuya da wannan tsohuwar Bus sosai. Kafin mu sauka jikina yayi likib. Muna sauka muka samu abun hawa ya kawo mu har ƙofar gidanmu. Ni dai ana isowa na sauka abuna, ɗan mabuɗin ƙofar na ciro a jakata na buɗe gidan. Dukkanmu ko wacce ita da mijinta suna da safaya ki da mijinta. Ɗakina na buɗe na shaga, ban zauna a falo ba na shige uwar ɗaki na rufo ƙofar garam. Zama nayi a bakin gado, kamar am tsikareni na miƙe. Cikin ƙarfin hali na buɗe akwatina na soma loda kaya, ina jin Gwadabe yana kiciniya da fantimotan Laila . Da gudu Toye ya shigo yana dariya, rungumeni tsam yayi. Tunda muka tafi Takai sai yanzu da muka dawo gida yaron ya sake. Dariya nayi mishi nace dashi. Keeni ( Menene)? Na tambayeshi da yare. "Kiyasi (Ba komai) Ya faɗa cike da nishaɗi. Muna cikin haka Gwadabe ya shigo da sallama. Hirar sama data ƙasa na haɗe. Ku meye shawarar da zaku ba Iyabo. Shin ta zauna da Laila a ɗaki ɗaya. Ko kuma tayi tafiyarta su Babala burinsu ya cika, shin inta koma gidan kuna ganin zaman zai mata daɗi. Sannan inta zauna tare da Laila me zai faru? Ina saurarenku MRS BUKHARI https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Lamba ta huɗu (4) *(SANARWA DUKKAN WAƊANDA SU SAYI WANNAN LITTAFIN TAMKAR SUN TAIMAKAMA MARAYUNE DA IZININ ALLAH. DOMIN KUƊIN KAI TSAYE ZAI TAFI ASUSUNMU NA GIDAUNIYATA MAI SUNA AMILA FOUNDATION NE. GIDAUNIYAR TAFI ƘARFI WAJEN TALLAFAMA MARAYU, DA TAIMAKON MARASA LAFIYA, SAI KUMA TALLAFAMA ZAWARAWA DA JARI MUSAMMAN WAƊANDA MIJI YA MUTU YA BARI DA ƳAƳA. SIYAN WANNAN LITTAFIN TAMKAR TALLAFAMA MARAYU DA IYAYEN MARAYUNNE. KUZO MUYI TARAYYA AKAN AIKIN ALKHAIRI)* *( KAR KU MANCE INA SAIDA TURARUKAN WUTA DA HUMRORI, DA DUK DANGIN ƘAMSHI MASU INGANCI NA MATAN KANURI. KANURI MUNE ƘAMSHI MEDUGURI GIDAN ƘAMSHI)* Ƙur yai mun da idanunshi wanda suka kaɗa su kai jawur. "Toye Wa Nibi ( zo nan)" Da gudu Toye ya je wajenshi. Murmushi yayi mishi yace. "L'o pade Anty re ( Je ka samu Antynka) Ya turashi zuwa falo. Yana fita Gwadabe ya mai da ƙofar ya rufe. A gabana ya tsugunna. "Ifemi (masoyiyata) me kike shirin yi, ɗakin ki kike son bari, Gwadaben naki kike son gujema? Duk irin juriya da gwagwarmayar da muka sha a baya bai sa mun rabu ba, sai dan akan Laila banzar bazara?. Ifemi ( Masoyiyata) kema kinsan dole zanyi wani abun ko dan samo mana mafita. Na fiki jin zafin tawo da Laila da mu ka yi. Iyabo kar ki yarda shaiɗan ya rinjayi zuchiyarki. Ki tuna Gwadabe ne naki wanda kikai mishi Alƙawarin mutuwace kaɗai zata iya gibtawa a tsakaninki dashi, ki rufa mun asiri ki zauna a ɗakinki" Shiru yayi yana jiran abunda zance. Gwadabe a gaskiya bazan iya zama da Laila a ɗaki ɗaya ba. Bayan tana ɗakin mijinta ma bata dena turo maka da saƙonnin ƙauna ba. To ka sani in ba baka san na san sabida kai Laila ta kaso aurenta ba, to na sani. Dan haka bazan zauna da kishiyata ɗaki ɗaya ta gama gane mun sirrina ba, in aurenta zaka yi basai an turota yimun c.i.d ba." Yanda nake maganar ina haki yafi komai ɗaga ma Gwadabe hankali ƙuri yayi mun da idanu yasan tabbas naje maƙura dan tsakaninmu yi nayi ne, bari na bari. Kafin ya tuno lafazin da zai rarrasheni dashi akayo kiran wayarshi, ya zaro a aljihu. Oga Lurwanu naga an rubuta, shine ogan Gwadabe wanda yake ma karen mota. Da sauri ya ɗaga, murya a sanyaye yace. "Oga Lurwanu yanzu na shigo Kanon, zan tawo yanzu in sha Allah, an gama lodinne?" Daga cikin wayar Oga Lurwanu yace. "Ka hanzarta Gwadabe, an yi rabin lodi, ana gamawa zaku kama hanyar Ikko da izinin Allah. Karen motarka yana nan tare dani tuntuni." "To Oga Lurwanu abinda zan barma iyali fa? Wallahi ɗari ukune a jikina da zanyi kuɗin motar zuwa inda kuke. Kuma a gidan babu komai. Kasan lamarin sai godiya" Oga Lurwanu yace. "Wannan babu wata matsala. Kai dai ka tawo ɗin. Ko yaro ka ba saƙo ya ajjiyema Iyalan. Kai muke buƙata yanzu" A haka su kai sallama da juna. Yana sauke wayar a kunnenshi ya dubeni. Hawaye nake ta faman sharewa. "Iyabo gashi bani da lokaci a halin yanzu. Kina jina da Oga Lurwanu. Abinda zance miki shine ki tausayama masoyinki ki yi zamanki a ɗakin ki, ki toshe kunnuwanki, ki ɗauke idanuwanki daga gani ko jin komai. Dana dawo zan nema mana mafita, amman in sha Allah Laila ba zata zauna tare damu ba. Ki kuma kwantar da hankalinki Laila ba zata taɓa samun gurbi a zuchiyata ba. Ba zata iya ruɗata da komai ba, a gabana ta yi wasan ƙasanta. Ni naki ne ke kaɗai Iyabo. Nasan kishi ke nuƙurƙusar zuchiyarki. Kinga hanya zan hau, taya hankalina zai kwanta in na barki kika koma gida. Sannan ke kan ki in kin koma gidan wani sabon damuwarce kika jefa mu a ciki. In ci albarkacin soyayya haba tauntsun soyayya" Duk wannan kalaman cikin sigar so gami da rarrashi yake yinsu. Gabaki ɗaya sai jikina ya mace mus. Ance tsakanin mata da miji sai Allah. Duk da ina jin bazan iya zama da Laila ba. Amman ya kamata in ma mijina uziri tunda shima umarni aka bashi, kuma bazan so akan faranta mun ya saɓama wacce tai sababin zuwanshi duniyar ba. Ajjiyar zuchiya na sauke kana nace. Kana da girman daraja a guna. Kaje Allah ya tsare maka hanya. Ya kareka da sharrin ƙarfe da sharrin hanya. Allah yasa sai dai ka ajjiye motar da hannunka ba dai ta ajjiyeka ba. Allah yasa a soma a sa'a, Allah yasa ƙarshen wahalarmu ne yazo. Ka kular mun da kan ka Gwadabe, dan akwai tarin tulin maganganu marasa daɗin ji a kan ku direbobin manyan motoci, sunan masu sana'ar tuƙin manyan motoci yayi ƙauri, sun san sirrin ajjiye daduro ni bana zarginka amman ina tunatar dakai jin tsoron rabbissama wati wal ardi. Kar ka zama daga cikin irinsu dan Allah, duk da a ko wacce sana'a akwai nagari, akwai na banza." Murmushi yayi ya rungumeni dani da ƙaton cikina yace. "Kamar yadda kika faranta mun raina, Allah ya faranta miki kema. Mala'ikun Allah ku shaida na ɗaga ƙafafuna domin Iyabo matata ta shiga Aljanna" Dariya mu ka saka dukanmu. Ka hanzarta jiranka akeyi dai kar ka shagaltu" "Wallahi kuwa. To ni zan tafi, zan aiko da ɗan kayan abinci da kuɗin da zaki riƙe a hannunki. Ki kula da kanki da abinda yake cikin ki. Da zaran kin soma jin naƙuda ki sanar ma Bose, nima ki yi gaggawar sanarmun, Bara'u sai ya zo ya tsaya. Ballema ina roƙon Allah yasa sai ina nan zaki haihu. Sannan ki kula sosai, Laila ɓarauniyace ta bugawa a jarida, ko ɓera bai kaita iya sata ba, kuma bai fita dabarun iya sace abuba, har hannu take sawa a wandon jeans na maza a kasuwa ta yashesu, gidan biki ko suna kuwa sata take yi tamkar tana bacci dan sauki. In zaki je gidan aiki ki kulle uwar ɗakin ki kar ki sake ki bar mana ƙofa a buɗe. Dan komai ɗauka take yi" Sumbatata yayi a baki, tare da riƙo hannayena muka miƙe tsaye a tare. To in sha Allah zan kiyaye, Allah ya tsare. Mu je in rakaka" Tare muka fito zuwa falo. Laila na tsaye a gaban hoton aurenmu dake manne a falon. Na ci lace da gwaggwaro. Gwadabe ya sha rigar asheke da hular ashoke kai ka rantse beyerabe ne shima. Jin motsinmu ne yasa ta zauna a kujera mafi kusa da'ita. "Fita zaka yi ne Yaya Gwadabe?" Ta furta da zazzaƙar murya ba irin tawa ba, dan muryata tana da ɗan girma gami da kauri. "E tafiya zanyi ma. Ni sai na dawo. Iyabo ki koma ki kwanta ki huta zuwa azahar kya tashi ki yi wanka ki yi salla." Kafin in ce wani abun muka jiyo sallamar Uwani Tabalbalin ƙawata tun ta ƙuruciya, ƙawarda banda madadinta. "A maraba lale Tabalbalin kece a tafe? Ai kuwa kinci sa'a dawowar ƙawar taki kenan daga ƙauye" Cewar Gwadabe daya tari Uwani da fara'a sosai. Cikin dariya tace. "Gwadabe na Iyabo ikon Allah tsuntsun soyayyar daya tashi daga kan Debisi sai ya hau kan Ɗan hausawa. Fita zaka yi ne?" Dariya muka saka dukkanmu, wannan suna yaƙi fita a bakunan waɗanda suka san gwagwarmayar da muka sha kafin aurenmu. "Wallahi tafiya zan yi ma zuwa Ikko. Ya yaran, ina Hafizu Oga ba?" Dariya mu ka yi duka. "Hafizu na baroshi a majalisarsu" A wajen mu kai sallama da Gwadabe ya fita, mu kuma muka koma uwar ɗaki ni da Tabalbalin. "Ashe tafiya kuka yi Iyabo. Kaddai bikin ƙanwar mijinnan naki marar kunyar nan, wacce ta watsa mun miya a zani lokacin sunan Toye kuka je?" Zama na yi a bakin gado. Na yi shiru kawai dan batun zaman Laila na ci mun tuwo a ƙwarya. Zama Uwani Tabalbalin ta yi a kusa dani tace. "Akwai wata matsalar ne Iyabo? Nasan ai ba zata wuce irin wulaƙancin da dangin Gwadabe suke yi miki ba ko. Balle kunje ƙauye an shiga taron biki" Wallahi da shine ma da sauƙi Uwani. Ai kinsan Laila tsohuwar budurwar Gwadabe, ƴar uwarshinnan wacce kwanakin baya muka samu saɓani?" Kai ta gyaɗa tace. "Na ji na ji. Wacce take turo da saƙon batsa tana gidan wani ko, ai kece banza da baki zaune ƴar banza ba. Halan wani abun tayi miki a cikin taro?" Itafa ƙawata. Ana baki kina karɓa Tabalbalin" Bata labarin abinda ya faru nayi kab ina share hawaye. Uwani da ba dan in na koma gidanmu tamkar na tozarta aurena bane, da wallahi kafin Gwadabe ya dawo na bar gidannan." "A'a kar ma ki soma. Dan in ma kika je Iya Debisi sai ta kusan illataki banda kwakwazon da za tai ta yi miki, maƙotanku ma sai sun ji meke faruwa. Amman gaskiya kar ki kuskure ki yarda kici gaba da zama da'ita ɗaki ɗaya maganar gaskiya. Ba zata zo har ɗaki ta iskanta miki miji ba. Amman ko da wasa kar ki sake ki bar ɗakin ki, yo kin bata dama ta kwace miki miji cikin sauƙi kenan ma. Nifa dani Gwadabe yake Aure da tuni na seta kan ƴan uwanshi. Ki kwantar da hankalinki tunda Gwadabe yace zai samo muku mafita kema kinsan bazai barki haka ba. Ya kika baro Sakina da mijintannan nata mai barkwanci Bara'u?" Ajjiyar zuchiya na sauke nace. Suna lafiya lau Uwani, ya Hafizu da yaran?" Shiru tayi na ɗan lokaci tace. "Iyabo yau haka muka wayi gari ko lomar da zamu kai bakinmu babu wallahi. Yaran sai turasu gidan Hajiyata nayi nasan ko ba komai ba zasu rasa abinci ba, tunda Hajiya na yin ɗanwaken saidawa. To mu ɗin bamu ci komai ba, ga ni da ciki na wata uku ban baki labari ba, wallahi bansan ina da cikin ba. Ga hayarmu ya ƙare gobe mai gidan zata zo karɓar kuɗinta, ko ficika bamu ajjiyeba, babu wanda muka ba ajjiya. To shine na sha maganin zubar da ciki cikin ya zube yau ɗinnan, Iyabo bazan iyaba, Hafizu bashi da zuchiyar nema. Ni rayuwarma ta isheni Iyabo, Talauci masifane ƴan uwanka ma sai su gujeka su ƙi taimakonka" Kuka ta fashe dashi kawai. Ban hanata rera kukan ba, domin kusan ni na fita sanin zafi da raɗaɗin talauci da wayar gari babu abinda za'a saka a ciki. Tunda Hafizu da yana da rufin asirinshi direban ƙaramar motane yana lodin Kano to Gomber, da Bauchi. Motarshi ce tayi haɗari ta yi rugu_rugu. Har yanzu bai samu wata motar ba. Shi kuma ya ɗaurama kanshi girman kan neman wata sana'ar. Daga haka ya ɓige da zaman kashe wando. Shi yasa rayuwar ta ɗaure musu. Amman ni dama a haka na shigo gidan Gwadabe na sameshi. Dama bashi da cikakkiyar sana'a duk abinda ya fita ya samu yi yake yi kawai. Numfashi na ja kana nace. Kiyi haƙuri Uwani da sauyin rayuwa. Mu yi ta yi musu addu'a babu dare ba rana. Ubangiji rabbissama wata wal ardi zai bamu mafita, zamu ji daɗi a gaba komai lokaci ne. Tashi mu je mu hura wuta, ga ɗan abinci mun samo daga ƙauye, ko fara ce in dafa mana, ina da yaji, mai ne babu dai." Tire na ɗakko na zuba shinkafa ƴar hausa Gongoni biyar, Uwani ta karɓa ta fita. Kurfot ɗina na zaro a ƙarƙashin gado da ƙullin gawayin hamsin a kai, nima na fito tsakar gidan. Wuta na hura da leda, Uwani na zaune a kujera tana tsintar shinkafa tace. "Ji gidan shiru kamar ba shi bane mai tarin hayaniya da bataliya ba" Yatsana nasa a leɓena nai mata nuni da tai shiru sabida Laila. Dole mu ka zama kuramen dole. Tashi nayi na ɗakko tukunya na buɗe randata dake bakin ƙofa cike da ruwa na zuba ruwan a tukunya, na ɗaura a wuta. Ruwan na tafasa Uwani ta wanke shinkafar ta zuba. Alwala muka ɗaura dukkanmu muka shiga ɗakin. Da sauri Laila ta ajjiye kwanon samira dake ajjiye a gefe guda. Kallonta nayi itama ta kalleni. Kai na girgiza na nufi hanyar shiga ciki. "Am Iyabo a ina zan ajjiye fantimotaina naga kamar basu dace su zauna a falo ba" Kallonta nayi na ƙara. To a ina kike ganin ya dace ki ajjiyesu in ba falon ba?" Na bata amsa cikin danne fishi, dan ji nake wallahi kamar in dira a wuyanta. "A uwar ɗaki mana, taya zan ajjiye kayana a falo?" Ta faɗa a gadarance irin ta dangi miji dan halinsu ne wannan kam. Cikin cusa haushi nayi dariya nace. Haba Laila, ai uwar ɗakina mallakinane tafi ƙarfinki, iyakar taki a falo take. Uwani mu shiga ko?" Na yi shigewata ciki na bar Laila tana surutai ni bansan ma me take cewa ba. Abinci na zuba mana a tire. Na zuba na Laila a kwanon silver, na zuba ma Toye nashi. Wani ƙaramin kwano na jawo a ƙasan gado, ragowar manjan miya ne a ciki nama mance dashi na tsiyayama Laila da Toye ragowar na ajjiye a gaban uwani danta soma cin abincinta ma gaya abunta. Falo na fita da zummar in ba Laila abincinta na tarar bata cikin falon. Ajjiye mata nayi a inda na barta. Na jawo hannun Toye yanata wasanshi muka shiga ciki na zaunar dashi. Kabbarar Sallah nayi. Ina cikin sallah muka jiyo sallamar namiji. Uwani ce ta fita dan dubawa. Sai da na idar sai gata da leda mai zane, da kuma baƙar leda da kuɗi dubu biyu. "Saƙone Gwadabe ya aiko miki. Gwadabe akwaishi da ƙoƙari akan komai ma, gaskiya ki sake gode ma Allah. Gwadabe ya riƙe miki amanar ƙaunarki. Iyabo kar ki kuskura wannan mai idanu a tsakar kan ta rabaki da mijinki." Tabalbalin sai na dage da tsaiwar dare. Domin tsorona bansan da wanne irin shiri tazo ba. Nasan kyanta, ko farinta, da kyan durinta bazai taɓar ruɗar Gwadabe ba. Na yarda da irin son da yake yi mun. Kuma na yarda yana ganin kyauna a hakan da nake, ko babu komai yakan yabeni ya kurantani. Kuma yasan da'itan ya tsallaketa ya auroni. Ni dai da sallar dare zan dage kar su je su nemar mun miji ta hanyar asiri. Uwani ina cikin damuwa sosai wallahi. Ke dai mu ci abinci kinji. Muna hirarmu muna cin abinci, anan na ba uwani labarin abinda ya faru a cikin gidannan ranar da zamu je Takai, da kuɗin hayar da zamu soma biya. Uwani tayi mamaki ainun ta jinjina irin ƙiyayyar da dangin Gwadabe suke yi mun. Sai bayan la'asar Uwani ta shiga haramar tafiya. Shinkafa da taliya, da kayan miya, da ɗanyen kifi, manja, maggin da Gwadabe ya aiko yaro ya kawo duk sai dana ɗibar mata, na bata ɗari biyar. Bata tafi ba sai da ta ɗoramun miyar tumatur a gawayi, da kanta ta leƙa ta kai mun niƙan maƙota. Sai da na rufe uwar ɗakina sannan na rakota. Mun fito mun samu Laila tana cin gurasa da lemun koka kola, abincin dana ajjiye mata kuma ta tureshi gefe guda, ƴar ƙaramar rediyo ta kunna tana jin waƙat barmani choje, waƙar gwarne ikon Allah. Tana yi tana karkaɗa kafaɗarta. Wucewa muka yi jiki duk a sanyaye. A sanyaye mu kai sallama da Uwani tana sake jan kunnena kar in kuskura in bar gidana sabida wata. Ko dana dawo ban shiga falon ba, a tsakar gida na zauna ina tsintar shinkafa ina shaƙar iskar ƴanci. Dan da masu gidan na nan, da ananan ana zubar mun da habaici, gami da maganganun cin fuska marasa daɗin saurare. A taƙaice dai ko dana gama girkin dare na sake zuba ma Laila a wajen ta sake bar mun. Ta fita ta siyo tea da biredi. Ni ko tunda na janye yarona na shige ciki nasa sakata, ban sake sanin halin da Laila take ciki ba. Misalin ƙarfe goman dare sai ga kiran Gwadabe ya shigo wayata. Cike da zumuɗi da kewa na ɗauka. Daman a zaune nake dan tunda cikina ya tsufa ban fiye samun baccin dare ba. Allah sarki Gwadabe da yana nan da yanzu yana matsa mun ƙafafuna. Amincin Allah ya tabbata a gareka gwarzon gwaraza. Barka da hanya, da fatan kana cikin aminci?" Murmushi yayi mun yace. "Barka sa dare sarauniyar zuchiyar Gwadabe, da fatan kina cikin ɗakinki na sunna cikin aminci ko?" Farin ciki ne ya lulluɓeni bansan sanda na lumshe idanuna ba. Ina lafiya, sai kewarka dake nuƙurƙusar zuchiyata. Ya hanya fa?" "Ba daɗi hanya. Kin ganmu a Tafa mun tsaya cin abinci da Sallah. Shine nace bari in ji lafiyarki. Ina Toye?" Gashi nan yayi bacci. "To masha Allah babu dai wata matsala da Laila ta baki ko?" Baki na taɓe kafin nace. Babu wata matsala a halin yanzu. Amman abincin rana dana dare dana bata duk bata ci ba. Fita tayi ta sai abunda ranta yake so" Faɗa ya soma yi akan karma in ƙara saka mata abincin in nayi tunda abun iskanci ne. Ni dai nace. Ba za'ayi haka ba. Ai da duk take_takenta so take in ƙi zuba mata a kafa mun hujjar na hanata abinci ita da gidan ɗan uwanta. Kai dai ka yi tunanin nemo mana mafita kawai. Dan wallahi Allah bazan zauna da gansamemiyar bazawara kamar Laila ba." Dariya Gwadabe ya dinga yi mun yana tsokanata kan na fiye kishi. Nima da dariyar na bishi kawai. A haka mu kai sallama dashi. Bacci bai zo ma idanuna ba, ƙarfe sha ɗayan dare na ɗaura alwala a cikin bahun babba. Na raba dare ina neman tsarin Allah ga dukkan masu son cutar dani da mijina, da masu son ganin bayan auren. Na roƙi Allah yai mun katangar ƙarfe da Laila ya karemu da dukkan sharrin data kwaso. Gwadabe kuwa alkhairi duniya dana lahira na roƙar mishi. Sai zaman lafiya, da jin daɗi wanda bana gajiyawa wajen sake roƙa mana, kusan duk addu'o'in maimaicine ba dare ba rana. Sai dai yau na ƙarama adda'ar tsawo da wasu salon roƙon. Sai wajajen jefin assalatu bacci ya kwasheni ina daga zaune. Amman ana kiran sallar farko na buɗe idanuna. Yinƙurawa nayi na tashi na buɗe ƙofata na fito da bahun ɗina na fice. Laila na saman doguwar kujera tana bacci saye da wandon bacci iyakarshi guiwa, rigar wandan mai shara_ shara ne har kan mamanta ina iya ganowa. Gabana ya doka da ƙarfi, kifiyar kishi ta soki tsokar jikina. Kai kawai na girgiza domin nasan tabbas dama a rina. Laila da kyan sufa da launin fata take son Jaye Gwadabe daga gareni. Dan tana da kyau tubarkalla masha Allah. Kuma ko a ƙauyen ita idanta a buɗe yake tar. Fita nayi na kama ruwa, na ɗaura alwala na koma ɗakin. Dai _dai da farkawar Laila tana tsaye tana miƙa. Na ƙarema wandon baccinta kallo shima shara_sharenne ina hango zaratan cinyoyinta farare luwai_luwai dasu. Ya kamata ki sani cewar nan ɗakin matar wanki ce, ba ɗakin aurenki ba. Wannan shigar a ɗakin mijinki kaɗai ya dace ki yita ba anan ba. Zan iya lamuntar komai, banda shigar banza mai nuna tsaraici, ki kiyaye sosai" Hararata Laila tayi tare da yin shewa tace. "Ashe ana tsoron iya inji ƴaƴan maiya. Babu rami me ya kawo rami Iyabo? Ashema baki yarda da nagartarki ba a matsayinki na mace ba." Murmushi nayi mata kawai domin bani da lokacin misayar yawu da'ita. Bayan na idar da sallah na yi azkar da adda'a, na jima sosai ina tunanin yanda ƙarshen zaman Laila a cikin ɗakina zai kasance. Ta yaya, kuma ya za'ayi tabar ɗakinnan alhalin Babalace ta bata umarnin zama, kuma dani da Gwadabe duk a ƙarƙashin ikonta muke. Wata zuchiyar tace. "Ai matsawar ba barin gidan kikayi ba Iyabo. To tabbas Laila babu inda zata fita taje. Babu makawa Gwadabe sai ya aureta. A daddafe na miƙe na shiga gyaran ɗaki, sai da na kintsa komai, na fitar mana da wankin kayayyakinmu na soma wankewa inayi ina rera waƙar yarbawa, amman wani shashe na zuchiyata a cike yake da tsoro da fargabar zamana tare da Laila. Kafin takwas na safe na gama komai har shara da wanka duk mun yi. Abinci na ɗunɗuma mana, kamar jiya na sake zuba ma Laila nata dai na dire mata. Ina gama karyawa na fito cikin shiri, na yi kaye_kayen kayana masu amfani na kulle uwar ɗakina. Laila na falo tana cin abincin dana ajjiye mata na yi ficewata ina jaye da hannun Toye, har zuwa bayan layinmu gidan da nake yin aikin shara, wanke_wanke, da goge _goge, sai wanki amman injinne yake wankewa, ya ɗauraye, ya busar gogewa ne dai nawa, sai in jera a sib, sai kuma girki amman shi ba ko da taushe bane. Babu wanda yasan ina yin wannan aiki, domin yana daga cikin sirrinmu ni da Gwadabe. Matan gida dai suna gutsiri tsomarsu akan fitar da nake yi tun safe, bani zan dawo ba sai azahar, har Gwadabe Yaya Hambali ya tara da zancan dan a tunaninsu gantali nake zuwa kawai. Yaya Haula kuwa cewa tayi bin gidajen maƙota nake yi yawon tsogumi, dan babu wanda ya kai yarbawa gulma da munafurci a cewarta. Da sallama na shiga madaidaicin gidan. Matar gidan tana ciki, dan na hango ƙofar falon a wangale. Bayan sallama kai tsaye na shiga falon. Tana zaune tana duba wasu kayayyaki da take ta warewa na maza da mata. "Yauwa Iyabo ashe kin dawo. Kar ki so kiga yanda wanki ya taru mana, kinsan yara da ɓata kaya" Dariya nayi cikin girmamawa da ɗan risinama wanda kake mutuntawa wanda ya zama ɗabi'a mai kyau ga ƙabilar yarbawa nace. Ina kwana Alaja ya yaran?" "Lafiya lau, an yi biki lafiya dai ko? Yau da Toye akazo bai je makaranta bane?" Wallahi kuwa bai je ba sai dai zuwa ƙarshen wata. Wannan kayan har da su a wankin Alaja?" Na tambaya ina kiciniyar kwashesu tace. "A'a kayane muka fitar na kwalima, za'a tura ƙauye a buhu zaki zura mun su. In akwai wanda kike so sai ki ɗiba" Baki na washe nace. Ahhh irin na yarbawa" Alaja nima inaso, bari in tsakura tunda mabuƙatan muna da yawa. Amman duk sanda akayi a dinga cira mun. Alaja tace. "To ki kwashe duka wannan na matan ki bar na mazan, ai ban gama kwaso kayan ba ma" Ba shiri na tsugunna ina ta faɗin. Ahh_Ahhh_Ahh Alaja na mazan ma inaso in da hali, zan bama mai gidana shima yana da ƙarancin suturu' Shiru tayi tana kallona, mamaki na bata ko tausayina taji sai Allah, sai da ta sauke ajjiyar zuchiya tace. "To ki haɗa duka ki kwashe, zan fito da wanda na ware a ɗakina sai ki zuba mun a buhu. Akwai takalman maza ƙafa biyu a dokin ƙofa ki haɗa dasu in zai ma me gidan naki, ni zam shiga ciki." Ahhh Olorun bukun fun o ebi re ( Allah ya albarkaceki, ya albarkaci iyalinki) Na faɗa da yaren yoruba. Na fassara mata da hausa dana tuna bata jin yaren. Da "Ameen_Ameen" ta amsa ta yi shigewarta ciki. Bayan na tattare kayan na shiga aikin share_share ka'in da na'in. Ina yi ina wanki a injin. Bayan na ƙalƙale ko ina kuma sai na shiga ɗakin yaranta, sai da na goge kayayyakin dana wanke tas kafin na miƙe lokacin anata kiraye_kirayen sallar azahar. Na jera na yaran a sib ɗinsu, na Alaja kuma na kai mata ɗakinta na saka mata a sib. Na gyare mata ɗakin tas. Kafin nayi salla kuma. In idar da sallah sai na tsinci kaina da rashin aha'awar komawa gida. Sai na tsiri gugar kayan da Hajiya ta bamu, tunda a wanke suke, sai ƙamshin turare mai daɗi suke yi. Dana gama wajajen biyu da rabi dai dole na fito daga ɗakin yaran ina riƙe da buhun kaya da Toye. Robar da take zuba mun abinci ta miƙo mun, da wata farar roba babba mai murfi tace. "Miyar ganye ce a cikin robar nan, ta ɗan jima a firji ne bazan iya amfani da'ita ba bansan ko kina so ba?" Karɓar ledar nayi nace. Inaso Alaja. Aidupe ( Nagode) Nayi mata sallama muka kama hanyar komawa gida. Ga buhu a kaina, ga leda a hannun hagu, ga Toye ina riƙe dashi, ga uban ciki mai tsini a gaba, ina tafe da ƙyar duk jikina ciwo yake yi mun. Da sallama na shiga gidan, tsakar gidan tsit kamar ba gidan hayaniya da shewa ba. Turus na tsaya a daidai tagar ɗakina bakina a sake, furucin Laila na ƙarshe a waya ne ya daki kunnena. "Ai in sha Allah na shigo kenan sai dai ta fita ta bar mun ɗakin, Gwadabe nawane halak malak" Sai ta saki Dariya. Murya a daƙile nace. Salamu Alaikum. Nasa ƙafa na shiga, tayi saurin kashe wayar da take yi. Na ƙare mata kallo da kyau. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI. Lamba ta biyar (5) Saye take cikin shuɗiyar atampa, ta ci kwalliya da jan baki da hoda, fararen idandunanta rambaɗe da kwallin daya sake fito da hasken fatarta. Sai wani ƙamshi take yi ita da falon. Haƙiƙa na tsorata da Laila da muguwar nifaƙar dake tafe da'ita. Amman in ta san wata ai bata san wata ba. Wanda ya riƙe Allah shi ke da gagarumar riba, nasara tana biye dashi. Dan duk nisan jifa dole ya dawo ƙasa. Kallon dana cikata dashi shi ya jefata cikin taraddadin daya kasa ɓoyuwa a fuskarta. Murmushin dole na sakar mata na yi shigewata ɗaki, na zauna daɓas a kan gado ina sauke numfashi kawai. Tagumi na zuba ina tunani. Na jiyo murya a falo kamar ta Burodami Debisi. Da hanzari na leƙo ai kuwa shi ɗinne a tafe da abubbuwan arziki. A guje Toye yaje ya ɗafeshi, shi kuma yayi maza ya rungumeshi tsam a jikinshi. Ɗagowa yayi ya ƙuramun idanunshi, nima shi nake kallo. Burodami barka da zuwa" Na faɗa tare da ƙoƙarin kawar da kallon da yake yi mun. Hijabi na zura , ban fito ba sai da na zuba mishi abincin dana dawo dashi daga aiki. Jallof ɗin taliyace ta ji bushasshen kifi, na zuba ruwa a kofin roba, na ɗaura a tiran roba, sai na fito. A gabanshi na dire tiran, na sake komawa na zubo ma Laila da Toye abincin bai yi ragowa ba, ga raina ya biya ina fatan Burodami Debisi ya ci ya rage in samu in lasa. Miƙoma Laila abincinta nayi, Toye ma na zaunar dashi a leda ya soma cin nashi. Ekabo Burodami ( sannu da zuwa Yaya) Ya gida, wa ni Iyawo re bawo ni ebi re? ( Ya Iyaninka) Murmushi yayi mun yace. Awon ti wani ol atanran. Bawo ni o se wa ( suna lafiya, ya kike?) Ohh mowa daa_daa ( lafiya Ƙalau) Ga abinci kaci karya huce. Abincin ya kalla nima ya kalleni, saurin kawar da kaina na yi gefe guda. Murmushi yayi tare da girgiza kanshi. "Ba zama nazo yi ba. Kuma in naci abinci anan, in na koma gida Emisi ba zata ji daɗi ba in nace mata na ƙoshi, dan na barota tana ta faman dakan sakwara" Wani yawu ne na jarabar kwaɗayin masu juna biyu ya tsinko mun jin an ambaci sakwara, muƙut na haɗiyeshi kawai, dan bani da yanda na'iya. "Ga TV da dvd, da kafet na kawo miki, na sauya ma Emisi kayan ɗakine shine na raba muku tsofaffin. Yanzu haka daga gidan Simbin Maman Kokodeen nake na kai mata labulaye da kujeru" Har ƙasa na tsugunna ina ragargazo mishi godiya, dan nayi farin ciki sosai, a cikin gidan ni kaɗaice bani da kayan kallo. Wataran matan gidan suna haɗuwa a ɗakin mutum ɗaya su harhaɗa kuɗi a yo renting ɗin kaset sai dai in jiyo sauti, muna dai da rediyo da muke sauraren labarai, harma wataran in saka kasetin waƙar yarena, dan Allah yayi ma yarbawa baiwar iya waƙa da son rerata, dan ko karatu zamu yi da waƙe muke yinshi, gamu da son sha'ani a taru taci asha ayi ashobi. Dubu biyu ya zaro ya ajjiyemun mu kai sallama ya fice. Kinkimar komai nayi na shigar ɗaki, na dawo na ɗauki abincin nayi shigewata, Laila na zaune bakan a zaune tayi tsit da halama saƙa take yi da mugun zare a ranta. Da daddare Gwadabe ya kirani mu ka ɗan taɓa hira ba mai yawa ba dai haka, yai mun albishirin ƙila jibi ko gata ya dawo da izinin Allah. Fatan alkhairi nayi mishi, tare da samun alkhairai. Washe gari ma kamar jiya ina gama komai na tafi wajen aiki abina. Ina dawowa tun daga bakin zaure na fahimci masu waje sun dawo mai tabarma dole ya naɗe, dan muryoyinsu har waje nake jiyosu ana mayar da yanda akayi da yanda za'ayi. Da sallama na shigo amman babu wanda yaji balle su lura da shigowar tawa. Karab a kunnena na jiyo Laila tana faɗin. "Ai ku baku ga irin kallon soyayyar da take ma farkan nata ba. Wai ni zasu ninke baibai. Ya kawo TV da dvd harma da kafet ƙato, ga kuɗi fa. Bai tashi zuwa ba sai da ta ga ba idanun Gwadabe" Yaya Haula tace. "In banda abinki Laila yarbawa ai sun saba iskanci wannan ba wani abu bane. Su da suke zaman wa jo ko, yarinya tana gaban iyayenta saita koma ɗakin saurayi, wai da sunan gwajin mahaifa, sai ya ɗirka mata ciki zata dawo gidan iyayenta. Kiga anata murna abu yayi kyau zata auru. In kuwa juyace shikenan an shata musulla. To su da suke haka har dan tsohon kwarton Iyabo ya biyota ɗakin aurenta wani abunne?" Ƙirjina take naji yana fat_fat_fat take numfashina na soma jin yana karkatsewa. Ban yi aune ba na jiyo muryar Gude tana cewa. "A can gidansu ma fa ɗakinsu ɗaya akace, tare suke gwamutsuwa su yi baccinsu, kinsan yarbawa dai sai a hankali basu cika hankali ba. Ni dai na rasa uban abunda Gwadabe ya gani a jikin beyerabiya wacce ƴar uwarshi Bahaushiya bata dashi. Ita ba kyauba, sai gandar baki da kayan ɗuwaiwaka ɓaka_ɓaka iyakar abinda matansu ke dashi kenan fa" Dariya suka saka dukkansu. Da Suwaiba muka haɗa idanu ina tsaye kasaƙe ina jin irin sharrikan da ake bina dashi. "Ahh kin dawo ne Iyaa Toye shine ba ko sallama?" Ta kula ni ne domin ta ankarar da abokan gulmar tata tai musu isharar wanzuwata. Ai kuwa sai su kai kamar ruwa ya cinyesu kawai. Hmmm e nadawo, ai nayi sallamar hira ce tayi daɗi shiyasa baku ji ni ba. Sannunku da hanya." Ina kaiwa nan na yi wucewata zuwa ɗakina. A saman kujera na zauna ƙirjina na soya mun. Da ƙyar na iya sa abinci a bakina, salla ma a daddafe nayi, kawai sai na ji na zama marar lafiya gaske. Sai tubka da warwara nake yi a zuchiyata hakanne ya hana ni sukuni da numfashi me kyau. Tun dawowar su Yaya Haula daga Takai, al'amuran gidan suka sake jagwalgwale mun. Sabon gulma da tsigudidi aka buɗe sabo. Laila kuwa irin ado da kwalliyar da take yi yana firgitani sosai. A tsakar gida suke wuni gulma da shewa, a gabana suke yi ma Laila adda'ar samun damar warce zuchiyar Gwadabe, tana amsa musu da Ameen. Ranar da Gwadabe ya faɗamun zasu shigo Kano da safe ina zaune ina wanki a ƙofar ɗakuna, ina ɗan waƙe_waƙenmu na yarbawa. Baban Nazifi ya fito daga banɗaki, dake banɗakin gidan a kusa da ɗakinmu lungun yake. Har ya wuce sai ya dawo da buta riƙe a hannunshi. "Wadannan randunan naki, da gayyar tarkacen robobinki, da wannan kwantenar da kike girki a ciki sun tsushe hanyar wucewa ban ɗaki. Sabida haka ki tattare komai a wajen ki sam inda zaki ajjiye, irin wannan tarkace suke lalata gida. Yana gama faɗar hakan ya wuce yana mita. Sukairaju wanda fitowarshi daga ɗaki kenan yace. "Yaya Hambali magana kake yi ne?" Ya tambayeshi. Cikin ɗaga murya dan in ji yace. "Da wannan masu kwalo_kwalon nake yi, kasan yarbawa da ƙazanta gasu ta tarin shirgi, ca nayi ta kwashe randunanta sun tare hanya." Harisu dake ɗaki sai ya amsa da cewa. "Yaya Hambali ai nima fa na jima ina son ince tarkacen lungun su Gwadabe yayi yawa, in zaka je banɗaki sai ka ta ture bokatai kafin ka wuce" Kaina na sauke ƙasa kawai. Gabaki ɗaya akan wannan maganar sai da kowa ya tofa albarkacin bakinshi. Ni dai da zafin zuchiya na gama wankina na nufi bakin rijiya zan ɗebi ruwa. Laraba ƙanwar Nazifi ƴar Yaya Haula kenan, tana bakin rijiyar tana ɗiban ruwa. Laraba ɗan zuba mun ruwa guga biyu nayi ɗauraya bayana ya riƙe" Ai ina rufe Baki Suwaiba ta iso inda muke da bokatanta da bahunanta itama zata ɗebi ruwa. Da safe duk matan gidan muke ciccika kayayyakin aikinmu, da randunanmu da ruwa. Buɗar bakinta tace. "Harda su kaza acin danƙo. Akanme yarinya uwarta ta sata aiki, zaki dakatar mata da aikin da aka sata kice ta zuba miki? Laraba in kin gama bani gugar" Ina tsaye Laraba ta gama jan ruwanta ta tsab sai ta miƙo ma Suwaiba guga. Ni ko nasa hannu na warce gugar a hannun Laraba. Na zura a rijiya. Suwaiba ta nemi kamani da kokawa a bakin rijiya, ai kuwa na dubeta nace. In ki kai wasa zan miki hajijiya in jefaki cikin rijiyarnan Allah, ki shiga taitayinki ba fa tsoro nake ji ba, ina dai son mu zauna lafiya ne. Da sauri Suwaiba ta matsa dan ni ɗin ƙatuwace tubarkalla masha Allah, kun dai san matan yarenmu akwai ƙiba babu laifi, gani da mazaunai a sama ɓaka_ɓaka masha Allah. Nan matan gida su kai mun ca a kaina, kowa na tofa albarkacin bakinshi, Gude har tana zunguremun kaina. Mazajen gidan a lokacin sun fita nema. Ni dai har na gama kab aikina na tsakar gidan, basu dena kwashena iyayena da dangina albarka ba. Ina shinfiɗa kafet ina hawaye harna gama shinfiɗawa, na saka tv da dvdn a inda ya dace, ɗakin sai ya sake sosai. Randunana na kwasosu na saka ɗaya a bayan ƙofar falo, ɗayar a uwar ɗaki, bokatan na ɗaurasu akan randar falo, bahunan kuma na ɗaura a saman randar uwar ɗaki, na fita na share wajen tas na shigo ciki. Duk fa wannan aikin ina jin ciwon mara da nake kyautata zaton haihuwace. Ina ninkin kaya na ji ciwon na ƙaruwa mun, ina jiyo ɓuruntun Laila a falo. Waya na ɗaga na kira Uwani Tabalbalin ,da Bose na sanar musu ina naƙuda, Bose kuma ta kira gida ta sanar, a cikin ƙasa da awa guda sai gasu dukkansu afujajan. Gashi ko reza bamu ajjiye da sunan haihuwarba, ta abinda zamu sa a bakin salati muke yi. Zaman dirshan nayi a ƙasan leda, sai zufa nake yi, ina ɗan nishi sama_sama su nai mun sannu. Ana cikin haka sai ga Yaya Mulka matar Burodami kokodeen, babban ɗa a gidanmu ta iso. "Yaya jikin nata Bose? " "Gashi nan dai tana ta fama, ko dai zamu kaita asibiti ne? Ƴan biyu ne fa a cikin ina tsoro" Ni da naketsakanin rayuwa ko mutuwa na shiga ɗaga musu hannu, ina musu nuni da su barni bazan je asibiti ba. Amman da ciwon yai tsanani gashi harna soma galabaita, babu shiri suka ɗaukeni, Burodami kokodeen ya zo da mota ƙofar gida. Matan gidanmu sai gani su kai an rirruƙoni mun fita. Sai faɗi suke "Au naƙudarce mu da muke cikin gida bamu sani ba, sai danginki kika kira? Yarbawa munafurci a jininku yake. Wannan ai iskanci da rashin daraja dangin mijine" Bansan wacece ta yi maganar ba, amman babu wacce ta tanka mata. Uwani maza je ki rufo mun uwar ɗakina. Na ƙarashe faɗe ina nishi. Tabalbalin:. A guje ta shiga gidan, tana shiga ɗakin Iyabo taga matan gidan a ɗakin cirko_cirko. Turus tayi da ta gansu, suma kansu sun dibibice da ganin Uwani. A zatonsu babu mai dawowa, sun shigo gulmar ganin gyara. Tsaki Uwani tayi ta shige ciki tare da cewa. "Aikin banza wallahi duk matar dana fito na sameta uwarta zanci danni ba Iyabo bace." Karo taci da Laila a cikin uwarɗakin gaban sib ta ɗauko sabuwar atampa tana hannunta. "Sata ce ta shigo dake ɗakin kenan? Iko sai Allah wai na kwance ya faɗi. Amman dai su Kulu anyi asara, an yi faɗuwar baƙar tasa, ko kuma ince ƙarkon kifi daga ruwa izuwa wuta, ayi dai mu gani in tusa zata hura wuta." Laila kuwa ba bakin magana ai da kunya an kama uwar miji na sata a ɗakin suruka. Fisge Atampar Uwani tayi. Sum_sum ta fice, Uwani kuma ta rufo ƙofar ta fito ba kowa a falo, tsakar gidanma data fito duk sun yashe. Abundai ba haka akaso ba, wai an yi gulmar uwar miji ta ji. Tana shiga motar suka ja sai asibitin nasarawa." Asibitin Nasarawa. Da taimakon Allah, na haifi yarana biyu, mace da namiji da kaina, sai ƙari da akaimun kaɗan. Tubarkalla yaran manya kamar ba ƴan biyu ba. Sai dai fa ina sauka ma'aikatan kiwon lafiya suka soma tambayar dangina kayan da za'a saka ma jarirai, da abubbuwan da ake buƙata. Ko allura bamu da'ita. Burodami kokodeen ne ya ba matarshi Antimi Mulka kuɗin dukkan abinda ake buƙata aka kawo babu ɓata lokaci. Cikin ƙasa da awa guda yarana an kintsasu tsab a cikin seti me ruwan toka, sun yi kyau sosai. Ɗakin hutu aka dawo dani. Da iyaa Debisi na soma haɗa idanu, tayi kicin_kicin da ranta, da gani kasan ta cika ta batse ƙiris take jira. Ko ma dama can haka take, kullum a cikin faɗa da kumfar baki take. "O ye koju ti e ( Kinji kunya) Ki duba kin haihu a wulaƙance, babu mijinki, babu dangin mijinki, babu kayan jarirai, ba kuɗin asibiti, jibi ramarki. Da ace kinji abinda aketa faɗa miki daba haka ba, da ɗan uwanki kike aure yarenku da kin fi haka daraja, kuma babu mai ƙyamatarki, ballema ya tsangwameki." Duk wannan maganar da yare take yi mun. Tana yi tana buga cinya, tana ɗaga murya tamkar faɗa, bil haƙƙi ita ba faɗa take yi ba maganarta ce haka, ko kuma ince mafi akasarin yarenmu suna da ƙarfin murya, da ihu a cikin magana. Ni dai bani da bakin cewa, dan nasan Gwadabe na ƙoƙari sosai, banso zuwa asibitin ba sabida gujema tashin hankali da tarzoma irin wacce ta afku lokacin haihuwar Toye, an yi ɗauki babu daɗi sosai. Dan ranar suna anci dambe an gode Allah. Burodami kokodeen ne ya katse Iyaa Debisi ta hanyar cewa. "Yarinyar nan Iyaa Debisi ya kamata a barta haka, ko dan rabon dake tsakani, ni ina ganin dukan yayi mata yawa" Miƙewa tayi tsaye, ta tafa hannu tace. "Ahhhh Ahhhh kokodeen Oya were ( baka da hankali)" Nan fa ta sake shiga wani babin, ta inda ta shiga ba tanan take fita ba. Shigo da yaran da ma'aikatan kiwon lafiya suka yi ne yasa ta yi shiru. Ɗakin kuwa Hausawa sai kallonmu suke yi. Iyaa Debisi take ta soma rera waƙa tana rawa na murnar zuwan jikokinta. Suma su Burodami kokodeen nan suka soma rawa suna mata tafi. Tana rera waƙar yarenmu ta musamman da akema ƴan biyu. Gabaki ɗaya ɗakin hankalinsu yana kanmu. Murmushi kawai nayi musu, Uwani kuwa sai zolayar Iyaa Debisi take yi dama sun saba. Taiwo Iyaa Debisi ta riƙe, Burodami kokodeen kuma ya karɓi Kahinde. Sai murna suke yi, domun a ƙabilarmu babban abune haihuwar ƴan biyu, mun ɗaukesu a matsayin wata babbar baiwa da Allah ya bamu. Kuma yarenmu su kansa yaƙinin rayuwar ƴan biyunnan mai albarka ce. Ni dai a haka baccin gajiya ya kwasheni, bani na farka ba sai jefin la'asar. Ƴan uwana sun cika asibiti danƙam sai tayani murna suke yi. Ga abinci iri_iri an kakkawomun. Burodami Debisi ya zubo mun amala da miyar ewodu, da miyar wake, da jar miya dukka, ga ganda haka_haka. "Ga abinci kici ko zaki samu ƙwarin jikin naki, gida zamu tafi" Karɓa nayi na mishi godiya. Ƴan uwa kuma aka shiga yi mun ya jiki, tare da murnar zuwan Taiwo da Kahinde duniya. ( Hassana da Usaini ) Amalata naci nayi ƙat na kora da kunun akamu me zafi, take naji na yi gyatsa mai ƙarfi, bana jin komai garau nake jina tamkar ba ni bace na haifi ƴan biyu ba. Wajajen shidan yamma aka sallamemu muka fito asibiti mota biyu. Duk tare muka ɗunguma mazanmu da matanmu zuwa gida. A tsakar gidan muka tarar da matan gidan kamar dai kullum ana zaman gulma da kace_nace. "Ahh ƴan biyu aka samu kenan? Kai masha Allah barka da arziki Iyabo." Cewar Yaya Haula. Yauwa sannunku" Iyakar abinda nace kenan. A ƴan uwana kuwa babu wacce ta kulasu, suma basu kula kowa ba, mu kai shigewarmu ciki. Mazan a falo suka zauna, mu kuma muka shige cikin uwar ɗakin. Anty Mulka tace. "Abun girkin ki na ganshi a falo. Anan zan dafa miki ruwan wankan ne, ko zan iya fita ƙaddararren tsakar gidan naku?" Sai da na ja numfashi nace. Zaki iya fita dashi ki sa ta gefen ɗakina, kafin Gwadabe ya zo ya kawo itace" Sai lokacin Bose tace. "To wai shi gogan bai san kin haihu bane?" Kafin in yi magana Uwani tace. "Na kirashi na sanar dashi. Yana hanyar dawowa daga legos ne, da ƙyar ma na samu wayar tashi ba sabis. Amman yace abokinshi Bara'u zai tawo daga ƙauye, duk abinda ake buƙata zai yi kafin shi ya iso, dan yace mun zasu iya kaiwa ma ɗayan dare basu shigoba, wata ƙila sai Asuba ma zasu shigo kanon." Tsaki Iyaa Debisi tayi tace. " Isokuso asan. ( Banza marar amfani)" Haƙiƙa naji zafi ainun, kuma maganar ta dokeni, ai ko banza Gwadabe uban ƴaƴanane." Anty Mulka ta fita bakinta a taɓe. Bose ta fita da zanin jini da muka dawo dashi daga asibiti, Uwani kuma ta ci gaba da mun gyaran ɗaki, sauran ƴan uwa kuma suka fita falo wajen su Burodami. Zuga su Yaya Haula su ka yi, suka shigo da sallamarsu, Iyaa Debisi ce ta basu izinin shigowa. Suna shigowa ta miƙe ta koma falo" "Iko sai Allah, Iyabo dama kunsan ƴan biyu ne a cikin naki, ko kuwa sai da kika haihu tukunna?" Cewar Gude uwar son jin ƙaƙa aka haifi mutum. A'a dama tun cikin ma yana wata huɗu da akayi mun sikainin akace ƴan biyu ne. Kun gansu mace da namiji. Taiwo da Kahinde kenan" Yaya Haula tace. "Au suma sunan yarbawan za'a liƙa musu, babu ko karar a saka sunan Mahaifin shi Gwadaben, ita kuma macen asa sunan Babala, sai wani Taiwo da Kahinde?" Uwani ce ta juyo tace. "Ba tana nufin sunan yarbawa za'a saka musu ba. Taiwo da kahinden yana nufin Hassana da Usaini kamar yadda muke cewa a Yaren Hausa. Tunda ai kunsan ba ko waɗanne ƴan biyu bane ake sake musu suna ba, ko a cikin hausawa " "To wannan ko dole a sake musu wallahi. Kun mayar da Gwadabe sai kace sususu kawai" Cewar Yaya Haula wacce da gani ta fusata. Uwani ba kanwar lasa bace na santa sarai shi yasa na katse zancan dan gudun kar su kira mun ruwa, dan ƙyas su Bose suka ji wata hayaniya zasu shigo ayi ɓatacciya, dan kowa cike yake da haushin kowa, sai kace ba Allah ɗaya muke bautama ba. Ya'isa haka Uwani dan Allah. Yaya Haula Gwadabe na da ikon ya zaɓama jininshi duk sunan da yake da buƙata. Ni bani da ikon sashi yayi abinda baya so. Ko Toye ma shi ya zaɓi ya saka domin yai na mahaifina Allah ya jiƙan rai takwara" "Tunda ya kasa yi ma nashi Allah ya ji ƙan ran takwaraba. Ai baki zo kin ganshi da mahaifinshi a raye ba. Dama yarbawa akuyarku ai tayi kuka wajen juya miji da jarabar bin baba lawo" Ta sake faɗa da karfi . Na riga da nasan tarzoma take son tayarmun, ayi rikici su sake kafa hujja akan jarabar yarbawa, da ƙin zaman lafiya. Haka dai suka fice a ɗakin bayan sun yi mun barka. Ni dai ban basu yaranba, dan a al'adarmu bama ba da yaro jariri ga mutane aita jagwalgwalashi. Suma sun sani tun a haihuwar Toye, kuma sun yi rantsuwar ko yara ɗari zan haifa ba wacce zata sake yinƙurin ɗaukar jaririn. Cikin ikon Allah a ƴan uwana babu wanda yaji kace_nace ɗin data faru, bayan fitarsu Uwani tace. "Iyabo sai fa kin yi da gaske dangin Gwadabe zasu iya barinki kici gaba da rayuwa a gidannan, wannan ƙiyayyar ta yi yawa. Wallahi ko ahalul kitabi ce ke ya kamata su sarara miki haka. Duk da su kansu Iyaa Debisi sunƙi su zubar da makaman yaƙinsu. Amman ɗazu fa kinsan ina dawowa rufe miki ƙofa da kikace. Su Haula suna falonki suna kallon ɗakin. Ita kuwa baƙar kadararcan a Uwar ɗakin ki muka ci karo tana miki bincike a sib, har ta ɗakko wata atampa mai ruwan malmo, kai gaskiya kina cikin wani yanayi." Shigowar Sakina ne ya katse mana hirar. Ah Sakina kune a tafe da yamma sakaliya haka? Maraba" Na faɗa ina dariya. Uwani tace. "Kaga uwar gida, kuma Amarya a gidan Bara'u, Sakina lale." Cewar Uwani. "Lale Uwani, ashe Iyabo uwar biyu an samu kai. Sannu fa mai jego. Bara'u yana falo yace a kawo mishi yarin zai musu huɗuba." Miƙewa nayi na saka mayafi, Sakina ta riƙe Taiwo ni kuma ina riƙe da Kahinde muka fito falon. Bara'u yana kujera shi kaɗai, babu kowa a falon, duk yanda akayi su Burodami kokodeen sun tafi gida ne, ko sun je su dawo. Sakina ta miƙa ma Bara'u Taiwo. Ina wuni Bara'u. Da wannan yammar Gwadabe ya taso ku?" "Haba dai ai Gwadabe ya wuci haka a wajena. Kuma dama muna shirin shigowa cikin garin jikin Babala yaƙi yanzu haka tana asibitin Murtala. Yaya Hambali da Sukairaju suna wajenta, amman ƙila ba gado za'a bata ba dai." Allah sarki, ai ban sani ba. Zan shirya in je zuwa bayan magriba in dai basu dawo ba." Sai Sakina tace. "Ke da kike fama da kan ki kuma?" Bara'u daya fita sanin dawar garin yace. "A'a in dai akayi magriba sai ki rakata ta je ta dubo jikin ai dai ba za'ace bata nuna kulawarta ba ko ba gaskiya ba" Huɗuba yayi ma yaran da suna Hassana da usaini kamar yadda yace Gwadabe ya bashi umarni. "To yara na yi musu huɗuba da asalin sunayen da ƴan biyu suke zuwa dashi, wato Hassana da Usaini. Taiwo da Kahinde a yarenku kenan. Sabida haka a ɓangarenmu Hassana da Usaini suke. A naku ɓangaren kuma Taiwo da Kahinde Allah ya raya su da imani" Miƙo mun yaran yayi na amshi ɗaya Sakina ta amshi ɗaya muka shiga ciki. "Me za'a ɗaura na dare ne Iyabo magriba ta kawo kai ma?" Cewar Uwani kafin in bata amsa Iyaa Debisi ta shigo da ruwa a bawo na wankan yara ta dasa kujera. "Fun mi ni omo ( Bani yaron) Ta furta ranta a mugun haɗe. A sanyaye na miƙa mata ina fatan kar a kuma samun matsala makamanciyar ta haihuwar Toye. Uwani ai inaga ba sai an yi girki ba, ga Amala a kuka da faten wake, ai ya ishemu, gobe a ɗaura girkin." Nabata amsarta. Anty Mulka ce ta leƙo tace dani in je in yi wanka ta kai mun ruwan. Wanka nayi na gargasa jikina sosai na ji daɗi. Ina fitowa Su Anty Mulka suna shirin tafiya gida Burodami kokodeen yazo zai kaisu gida. Godiya nayi musu sosai, mu kai sallama suka fita ni kuma na koma ciki. Anan naga kayan abincin da su Sakina suka kawo mana, garin tuwon masara, kuka daddawa, busassun kayan miya, albasa, shinkafar hausa, da gyaɗar miya harma da man ƙuli jarka guda, da bushasshen kifi" Godiya nayi sosai gami da yaba ƙwazon Bara'u, ya kuma yi dace da macen da bata hanashi yin aikhairin sai ma taimakonshi da ƙara ƙarfafashi da take yi." MRS BUKHARI https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE. GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Lamba ta shida Shiryawa nayi cikin doguwar rigar Atampa, ɗaya daga cikin kayan da Alaja ta bani, atampar mai kyauce kuma tana da tsada da gani. Hijabi mai roba_roba na saka kalar atamfar sak. Na ɗauki Taiwo na goya, Kahinde kuma Sakina ta goya shi. Uwani zamu je asibitin Murtala Babala tana can bata da lafiya gara in je kar in yi wani babban laifin. "To sai kun dawo, nima ƙoƙari nake in gama gyare miki uwar ɗakin yadda ya kamata. Gobe za'a zazzo da yawa. A nan ma ni zan kwana gobe na koma gida Hafizu baya nan ya tafi Lahadin makoli mahaifinshi bashi da lafiya. Yaran kuma suna gidanmu " nace da'ita. To Shikenan ma, sai mun dawo to. Sakina muje." Shigarmu ward ɗin mata ke da wuya na hangi su Yaya Haula dukkansu a zazzaune a tabarma da mazajen nasu. Kallona suka shiga yi da suka hangoni. Sannunku Yaya Haula ya mai jikin?" Sai da ta taɓe bakinta tace. "Jiki da sauƙi" Gaishe da su Sukairaju nayi tare da yi musu ya mai jikin. Yaya Harisu cikin murtukewa yace. "Da'u ka kai su wajen Babala su gaisheta" Da'u yayi gaba muka bi bayanshi har bakin gadon Babala, tana zaune ta jingina bayanta da matashin filo. Yaya Halima kuma tana tsaye tana haɗa mata tea. Muna isowa Babala ta kawar da kanta gefe. Sannu da jiki Babala, ya ƙarfin jikin? Na furta muryata har tana rawa. "Da sauƙi" Ta bani amsa ciki_ciki. Yaya Halima kuwa nunawa tayi bata ma san Allah yayi ruwan tsaron mu ba. Gaisheta nayi tare da yi mata ya mai jiki. Babu yabo babu fallasa dai ta amsa mun. Da Sakina ne dai su kai fara'a. Sunto Taiwo nayi na miƙa ma Babala ita, tasa hannu ta amsheta, Sakina ta ƙara matsa da Kahinde. "Ba shakka gashi nan yara sun ɗebo ƙoƙon asali. Kamanninsu sak da dangin uwarsu dai kamar yadda Toye yabi sunanshi." Iyakar abinda tace kenan ta miƙo yaran. Raina ya sosu ainun ko Allah ya rayasu bata ce ba, balle ta yi musu adda'a a matsayinta na kakarsu. Yaya Halima kuwa ko kallo yaran basu isheta ba. Bayan na gama goyo ne ta kalleni sak tace. "Na ji saƙonki na gode da har kike tunanin mahaifinki ya fi mahaifin Gwadabe daraja a wajenshi. Burinki ya cika yaranki uku babu wanda Gwadabe yayi ma takwara a danginshi. Har ni da na ɗau jimirin renon cikinshi na wata goma ya kasa saka sunana ma ƴarshi. Taiwo da Kahinde ɗin dai da kika sanar, shima shi ya jaddada a matsayin sunan yaranshi. Ko da yake dama tuni kun gama tsarin komai tun ma yaran suna ciki." Baki na buɗe inason in ba Babala haƙuri amman sai ɗaga mun hannu tayi. "Kije kawai, bana son ganinki, bana kuma ƙaunar zamanki da Gwadabe, zuchiyata ba zata taɓa samun salama ba madamar kina amsa sunan matar Gwadabe abadan" Cikin razani da tashin hankali mai girma na shiga. Lokaci guda Gwadabe da aurenshi ya fice mun a raina kwata_kwata. Na yi alkawarin inayon arba'in zan tursasama Gwadabe sakina ko dan ya ga haske a rayuwarshi, domin na fahimci har abada Babala ba zata taɓa ƙaunata ni da abinda na haifa ba, wannan shi ake kira NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE. Ko Gwadabe bai sake ni ba, ni kuma zan fice a rayuwarshi.Wata wawuyar ajjiyar zuchiya na sauke a hankali na soma tafiya dan barin ɗakin. In sha Allah ƙarshen aurena da Gwadabe yazo, ko da kuwa soyayyarshi ita zata zam silar numfashina. Fitowa daga ɗakin ke da wuya, na jiyo Harisu yana zagina tare da ƙorafi kan sunayen yara da aka saka. Sai ji nayi na muzanta ko fita ma bazan iyaba. A tsaye Sakina ta iskeni. "Ki ƙara haƙuri dai Iyabo damo sarkin haƙuri. Mu je kinji" Da taimakon Sakina na iya fitowa, amman har muka isa guda ban iya furta ko kalmar A ba, sai ajjiyar zuchiya kawai nake saukewa. In sa abinci a cikina wallahi na kasa sabida tsabar damuwa. Sakina da Uwani sai aukin rarrashina suke yi, amman na kasa ce musu komai. Ni tunanina ya na ga samarwa Gwadabe sauƙi dan fishin iyaye masifa ne, nayi imani fishin da Babala take kwana ta tashi dashi akan Gwadabe shi ya hana shi yin arziki. Kullum cikin faɗi tashi yake, ta hana kowa ya taimaka mishi. Yaya Hambali shago gareshi babba a kasuwa da yake siyar da dabino da gyaɗa, buhu_buhu yake siyarwa yana da yaran shago sosai. Amman Babala ta hana shi ya ɗauki Gwadabe ko da a matsayin yaron shago. Yaya Harisu shi kuma mota yake ja zuwa ƙauyuka a haka ya sai wasu motocin guda biyu ya bayar anayi mishi hayarsu. Sukairaju kifi bushasshe yake saidawa a kasuwa, shine zuwa argungi, shine zuwa maiduguri, da Yawuri saro katan katan na kifi, kuɗi yake samu sosai da sosai Ɗan fodiyo kuma Kafinta ne kuma ogan kanshi ne. Da'u shi kuma Yaya Hambali ne ya buɗe mishi shagon sai da kayan masarufi dangin shinkafar hausa, gyadar miya, masara, wake. Duk wannan matakan sun haushine da taimakon Allah da taimako da jajircewar Yaya Hambali, domin Yaya Hambali guda ne harda ɓari ga ƴan uwanshi, yana musu tsananin so. Ina lokaci yayi da zan fita fit a cikin wannan ahalin, nima in je in yi rayuwa mai kyau. In ba haka ba bala'o'e iri_iri zasu iya saukar mana a sakamakon fishin da Babala take yi da Gwadabe. Abubbuwa nawa Gwadabe ya kama suka lalace, yayi sana'o'e a ƙalla iri huɗu karen mota shine na biyar. Amma tafiyar bata wani nisa sai abun ya lalace, ko mai gidanshi ya koreshi, ko a yi mai wani ƙazafi, ko na sata ko na ƙashin tsiya." "Iyabo ga tea ki daure ki sha, wala Allah ruwan nono yazo miki. Kinga Taiwo da Kahinde kuka suke yi baki ma sani ba. Kar ki kuskura waccan munafukar ta falo ta fahimci kina cikin matsala, yanzu ta shigo. Surukar taki ma an sallamota tana ɗakin umman Nazifi." Hannu nasa na amshi tean hannun Uwani na sha, dan jikina har rawa yake yi tsabaragen yinwar da nake ji. Sakina ta miƙo mun Taiwo da take ta canyara ihu kamar wacce ake zare ma rai. Ga man zaitun da audiga Sakina bani in goge kan mamana in gwada musu ko zasu jawo ruwan yazo" Miƙomun Sakina tayi, na bi kan mamana na goge da man zaitun tas na ba yaran suka soma ja. Cikin ƙudurar Allah sai ruwan nono ya soma zuwa. Nan kuka yaƙare aka shiga tsotseni. A wannan daren bana ce na yi bacci mai kyau ba. Misalin ukun dare sai ga Gwadabe, a lokacin duk su Uwani suna kan gado sun yi bacci ya shigo. Ganinsu ne yasa ya koma falo, ni kuma na ɗebo jariran na biyo bayanshi, yana zaune a kan kujera. Laila kuma tana kwance tana bacci ta yi baje_baje cinyoyinta duk a waje. Miƙa mishi yaranshi nayi yasa hannu ya amshesu yana fara'a. "Maman biyu barka da sauka, ina fatan babu inda yake miki ciwo ko?" Babu, sannu da dawowa" Iyakar abunda na faɗa kenan shima ciki_ciki. Idanunshi yana kan yaranshi yace. "Ya dai akwai wani abu dake damunki ne, ko an yi wani abunne? Iyabo a yanzu ya kamata ace kin saba da komai. Ki toshe kunnuwanki dan abubbuwa da yawa zasu faru kafin ayi suna kema kuma kin sani. Yanzu haka nafi awa ɗaya da shigowa Babala naketa ba haƙuri tayi fishi wai ban mata takwaraba ita da mahaifinmu. Nace mata zan sake yin sabuwar huɗuba in hakan zai bata farin ciki. Amman taƙi fur tace mun in na sake ma yaran suna bata yafe ba, wallahi kar kiji......." Ɗan yatsana nasa a kan laɓɓana nayi mishi halama da yayi shiru, nuni nayi mishi da Laila dake kwance. Ai ba shiri ya haɗeye maganarshi. Mu ka ɗan taɓa hirarmu kaɗan, ya miƙo mun ledoji manya biyu, mu kai sallama dashi zai kwana a ɗakin zaure, ɗakin su Nazifi, Bara'u ma yana ɗakin. Da tunane_tunane na ƙarashe daren nawa, sai jefin asuba bacci mai nauyi sosai ya ɗebeni bani na farka ba sai taran safe lokacin ƴan uwana sun ƙaraso, har an yima ƴan biyu wanka sun fito ras dasu, dan Gwadabe ya kawo kayan jariri kala biyar biyar, sai nawa na fitar suna kala biyu, da takalmi da mayafi, sai sarƙa, dasu nabkin, da paints na yara, da man shafawa, da sabulu. Ɗayar ledar kuma kayan abinci ne a ciki. Ina farkawa Yemisi tace. " Lo we. ( Je kiyi wanka)" O dara ( To) Kawai na iya ce mata na ɗauki zani na lulluɓe jikina dashi na fita. Ina fitowa maƙotanmu suka soma shigowa barka. Matan gida kuwa babu wacce ta leƙo, sai aikace_aikacensu suke yi kawai. Bayan jama'a sun ragu sai na fita zuwa ɗakin Yaya Haula dan gaishe da Babala. A falon na tarar da Gwadabe da Bara'u gurfane a gabanta. Ɗan fodiyo yana gefenta yana ɓallo mata magungunanta. Gaisheta nayi da jiki, da ƙyar ta kada baki ta amsa mun. Ɗan fodiyo na gaishar kafin na gaishe da Bara'u da Gwadabe. Ni dai anan na tafi na barsu. Da tuwon masara miyar kuka da bushasshen kifi Uwani ta tare ni, harda tea mai madara, ina bacci Gwadabe ya shigo da kayan tea. Anty Mulka ce ta shigo ciki tace. "Wai Iyabo su dangiin mijinki basa zuwa taya aikine? Tun sassafe muke ta aiki a tsakar gidanku, amman babu wacce ta taya mu komai. Mun fitar miki da randunanki tsakar gida, wata bushasshiyar mace tazo tana faɗar maganganun banza, har tana dangantamu da ƙazanta. Mu fa ba zamu ɗauki irin wulaƙancin da sukai mana lokacin sunan Toye ba. Bga won ( ki ja musu kunne) sai in zaune mace ni yadda nake da ƙibarnan" Nan Bose da Kauliya suka ɗauka suma sai yare suke ta yi mun. Uwani ce tai ta basu haƙuri ni kam kuka na saka musu kawai. Ganin kukan nawa ne yasa su kai haƙuri. Tun ganin da naima Gwadabe a falon Yaya Haula ban kuma saka shi a idanuna ba. Da rana Iyaa Debisi ta aiko mun da farfesun kan akuya cikin kwano shi naci da rana, su kuma suka dafa taliya. Uwani na kira nai mata raɗar ta zuba ma Babala ishasshe a kai mata. Amman ko da aka kai sai dawo dashi Uwani tayi Babala tace bata cin abincin Yarbawa, da akayi tuwon dare ma na kuma sa Uwani ta kai mata, amman bata karɓa ba. Har magriba babu Gwadabe ba dalilinshi sai wajajen taran dare muna zaune dani da Sakina da Uwani suka shigo shi da Bara'u da ƴar baƙar ledarsu a hannu. Idanu ya zuba mun tare da lumshe su. Na fahimci akwai gajiya da tarin damuwa dake damun Gwadabe. Ko wanne halin zai shiga in na barshi oho, nasan Gwadabe yana sona so mai tsanini, duk da na fishi zurfi a soyayyar da nake yi mishi, jin Gwadabe nake tamkar shine mahaɗin numfashin da nake yi dan in rayu. Amman dole in fita daga rayuwarshi shima ya samu ya nutsa. "Ayi mun afuwa uwar biyu. Abubbuwanne su ka haɗu suka caɓe mun. Mun fita da Bara'u fafutukar yanda za'a samu na abincin suna da abun haƙiƙa a fita kunyar ƴan uwa." Murmushi nayi mishi nace. Babu komai, sannunku da dawowa ina wuninku?" A tare suka amsa duk aka gaggaisa baki ɗaya. Sakina ta tafi kawo musu tuwo. "Tamu ya kirani da magriba madam ɗinshi tana son tayi miki barka, yace ma ana gobe suna zata zo. Bari in kira ku gaisa" Kiran layin Tamu yayi bayan ya ɗaga wayar sai ya miƙo mun muka gaisa tare da yi mun barka. Daga ƙarshe ya haɗa ni da Ayashe itama tayi mun barka tare da faɗin. "Kayan fitar sunan ƴan biyu dana Maman ƴan biyu yana wuyana in sha Allah. Ana gobe suna zan tawo in zo ayi komai dani." Dariya nayi nace. Muna godiya Ayashe Allah dai ya bar so da ƙauna, mun gode ƙwarai" Mu kai sallama na miƙa ma Gwadabe, nan Tamu yake sanar mishi ya ɗauki nauyin rago ɗaya. Mun yi farin ciki matuƙa gaya. Sun jima a falo muna hirarmu gwanin ban sha'awa daga ƙarshe su kai mana sallama, suna fita muma muka tafi kwanciya. Haka dai ranaku sukaita tafiya, duk da kauce ma rikici da dangina suke yi sai da akayi rikici a tsakanin Anty Mulka da Yaya Haula. Wai an jiƙa tsakar gida da ruwan wanki, shine fa Yaya Haula tai ta zage_zage tun su Anty Mulka basu tanka ba har suka tanka. Akaita gwabza rikici har sai da manyan unguwa suka shigo akaita basu baki tukunna. Ni dai ranar naci kuka sosai sabida Babala har ɗaki ta shigo ta ƙaremun tanadi tas. Har ta gama babu wanda ya tanka mata, sai da tayi mai isarta ta fita. Ana gobe suna da yamma sai ga su Gwadabe da raguna tiƙa _tiƙa guda biyu sun ɗaure, da kayan cefanen suna niƙi_niƙi. Daf magriba Ayashe ta ƙaraso da yaranta biyu. Gaskiya ta gwangwajeni da ƴan biyu sosai. Shadda ta ɗinka mun taji aiki sosai, harda mayafi da takalm. Taiwo kuma bulawus mai tsada ta siyo mata irin mai takalmi da abun kai na yara, Kahinde kuma riga da wandon jins ta kawo mishi. Godiya na dinga yi mata. A ranar Bose, da Kauliya, da Anty Mulka a nan suka kwana. Washe gari asubar fari aka shiga aikin abinci. Da asubar Burodami Debisi ya kawo mana nama cikin leda mai zane, Burodami kokodeen kuma ya turo masu rumfa suka kafa runfuna biyu da kujeru. Yasa yara suka shigo da koka kola kireti huɗu. Ƴan uwa masu daɗi, ƴan uwa abun wuya wannan ya kawo nashi wannan ya kawo nashi sai kaga ashiri ya rufu ruf, a gaskiya ba yabon kaiba muna da hadin kai sosai. A ƙofar gida suka kafa murhun girki, masu Amala nayi, masu yin jallof nayi, ga nama jingin anata yankawa ana soyawa, wasu suna gyaran kayan miya. Tun asussuba ni da ƴan biyu muka yi wanka, ina ɗaki a zaune Bose tanai mun kwalliya ta kece raini. Ba yabon kai ba mu yarbawa mun iya kwalliya da sanin darajar kaya masu tsada. Domin mazan yarenmu basu san siyama mace ƙaramin zani ba, ko ashobi zamu fitar muna zaɓar mai tsada mu fitar. Domin matan yarbawa har adashe akeyi na musamman domin kece raini, ko wacce mace tana son asan mijinta na kulawa da'ita. Ko ni duk talaucinmu tun cikina na wata ɗaya nake zubin dashi a shagon Iyaa Beji me shagon atampa da lace ta bakin layinmu. Da kaɗan_kaɗan na tara kuɗin les ɗaya, sai naci gaba da tarawa, in ƴan uwana sun kawo mun ziyara sun ban kuɗi a ciki zan zari wani abu in zuba dashi, da haka na sake tara kuɗin leshi na karɓi lace biyu iri ɗaya na bayar da ɗinkin nawa a wajen Yemi, na gwadabe da Toye na bayar a shagon ɗinkin maza. Lace ɗinne a jikina tun sassafe nasa aka miƙama Gwadabe nashi shi da Toye dan tare suke kwana a ɗakin zaure. Sarƙa Bose ta saka mun a wuyana. "Wannan karon mai gidanki yayi ƙoƙari ba kamar lokacin haihuwar Toye ba. wannan lace ɗin da sarƙar babu laifi ba sui arha da yawa ba, ba sui tsada can can ba. Ga raguna manya_manya" Harara na doka mata, ta kwashe da Dariya ta doki kafaɗata. Dole nima na murmusa, dan Bose a lokacin da nake cikin matsi a gida sakamakon soyayya da Gwadabe, a wajenta kawai nake samun sauki. Yaya Haula ce ta shigo ɗakin da sallama tana wani gatsine, ta sha kwalliyarta da wata shadda mai maiƙo tayi kyau sosai, dan Baban Nazifi yana ƙoƙarin sosai a kan iyalanshi, bama su kaɗai ba harda iyalan ƙannenshi. Turus tayi data ganni na fito shar dani kamar ba ni ba, ba wata kwalliya bace a fuskar tawa ba, hoda ce sai jan baki, sai kwalli da Bose ta ziraramun, ko ja gira banyi ba sakamakon akwai gashi sosai a girata. Ɗan kunne da sarƙar da Ayashe ta tawo mun da'ita ta ba da gudunmawa sosai wajen ƙawata kwalliyar tawa, sannan dinkin buba ɗinkine dake fito da kyawun ko wacce irin mace, musamman masu jiki duma_duma irinmu, kwalliya da ado na fito da masu ƙiba ainun. "Iyabo gashi kayan yarinya na ɓangaren dangin miji." Ta dangwararmun da leda mai zane_zane. Kafin in yo godiya ta ƙara watso mun mugun kallo tace. "Na ga anata aiki babu wacce ta buƙaci ganinmu a wajen. Amman ki sani duk tsiya dangin uba sun fi power fiye da dangin uwa. Amman ke kinfi son duk abunki ƴan uwanki su tsaya a wajen, dan ku aikinku kenan ƙabilanci, tunda kika haihu ake yare a gidannan dan masifa." Murmushi nayi dan har ga Allah bana son cusa ma zuchiyata baƙin ciki a irin wannan rana mai albarka. Ai bansan basu neme ku ba Yaya Haula tunda ni bana wajen." Jijjiga kai tayi tace "Ai ba zaki sani ba tunda dai Gwadabe shi ya baki ƙofar raina danginshi. Babala tana gidannan a kasa zuwa a kiramu mu kama aiki a matsayinmu na dangin miji, ai shikenan hausawa na cewa sai bango ya tsage ƙadangare ke samun mafaka." Tana gama faɗar haka ta fice fuu kamar kububuwa. Ajjiyar zuchiya kawai na sauke na jawo ledar data dire mun. Riga ce ƴar ɗari uku uku guda biyu ta mace da na namiji, sai sabulu sanda biyu da omo mudu ɗaya shikenan abinda ke ciki. Bose ta riƙe baki tace. "Wannan kayan shine kayan dangin miji ke da kika haifa musu ƴan biyu? Lallai Anty Iyabo dangin mijinki basa ƙaunarki.. Ya isheni Bose ki barni in ji da abinda ke damuna dan Allah." Ina faɗar haka na miƙe zuwa uwar ɗaki, na tarar da Ayashe tana shirya Taiwo da Kahinde sun fito sun yi kyau sosai. Dubana tayi tana dariya tace. "Kai masha Allah mai jego kin fito shar dake kamar ba ke ba." Dariya mu ka yi dukkanmu. Simbi ce ta shigo niƙi_niƙi da buhu ta dire a gabana, Sai ga Taufiq shi da Lekan suma sun shigo da ghana most go. Yaran Burodami kokodeen ne Taufiq, Lekan kuma yaron Iyaa Kokodeen ne, Simbi shekararta goma sha takwas haka, wannan shekarar ta game sakandare ɗinta. Taufiq kuma yarone shekararshi sha biyu, yana jss 2. Lekan kuwa saurayine Buhun sobeniya ne na robobi, da kofuna, mafificin roba, moɗa da sauran kayayyakin roba mai manne da sikitar dake ɗauke da sunan Taiwo da Kahinde. Wanda ya ɗauki nauyin yi naga an rubuta Burodami Debisi Adebayo. Ghana most go ɗin kuma shaƙe take dam da kayan jinjiraye da atampopi , omo, sabulu da su nabkin. Hawayene ya gangaro a kumatuna mahaifiyata na tuno tana can ƙungurmin daji, babu waata hanyar da za'a iya sanar mata na haihu balle itama tazo ayi komai a gabanta. Duk da bani da maraicin uwa sam balle uba, Iyaa Debisi itace makwafin uwa a gareni, Burodami Debisi kuma shi ya zame mun makwafin uba. Shi yaita ɗawainiya da rayuwata har tasowata yanzu ma da nake gidan mijina bai fasa turo mun abun alkhairi ba, kuma yana kawo mun ziyara lokaci zuwa lokaci, duk da matarshi na tsananin tsantsar kishin kulawar da mijinta yake bani, sabida alaƙar data tafa gibtawa a tsakaninmu na soyayyar da Allah bai nufi shine uban ƴaƴana ba. Kafin ƙarfe takwas na safe tuni an gama girki tsab an zuzzuba a kuloli, An yanka raguna harma an gyara kayan ciki, kayan cikin dabba ɗaya nace a miƙa ma su Babala su soya da kansu kar suce an musu coge. Abinci ma ni da kaina na tsaya saida aka basu duk abinda ya dace, har sobeniyarsu nasa an cire musu Anty Mulka da Uwani suka kai musu har ɗakin Yaya Haula. Takwas da rabi Alfa Abdulsallam Abdulganiyu ya iso, ƙofar gida, zuwa lokacin ƴan uwa maza da mata duk suna waje a cikin rumfa a zazzaune. Gwadabe ne ya ratso cikin mata yana saye da leshi da hular ashoke, Kahinde ya riƙe Ni kuma ina riƙe da Taiwo, Ayashe da Sakina ne suka mara mana baya har zuwa ƙogar gida inda Alfa Abdulsallam Abdulganiyu ya soma wa'azi. A gabanshi muka gurfana, ya soma ragargazo ma ƴan biyu adda'a tare da roƙa musu alkhairan duniya dana lahira, tare da samun nasara gami da rayuwa mai tsayi, mai albarka. Duk wannan cikin yaren yarbanci yake yi, yanayi da waƙa dukkanmu muna amsawa da. Ameen" Muma cikin salon rerawa kamar masu waƙa. Yaran muka miƙa mishi ya shafa kansu yai musu adda'a ya miƙo mana su. Sannan ni yai mun adda'ar samun lafiyar shayar dasu cikin lafiya, Gwadabe kuma yayi mishi adda'ar samun tagomashi ta yanda zai ciyar dani lafiyayyen abincin da zan raini yarana cikin ƙoshin lafiya. Iyaa Debisi ta fito itama tayi nata addu'o'in, aka miƙa ma Babala abun magana, "Allah ya raya su da imani" Kawai tace shima sabida idon mutanene da taga sun yi yawa a kanta. Iyaa Kokodeen itama ta yi nata, su Burodami kokodeen da Burodami Debisi duk dai kowa yayi nashi.Daga nan kuma akayi adda'a kowa ya shafa. Sai Bose ta ɗauki kwano ta dinga bin mutane ɗaya bayan ɗaya sunata zuba kuɗi, mu kuma muka koma cikin jama'ar suna. Dangina rankatakab ɗinsu ankon atampa mai ruwan kunun kanwa ce a jikinsu maza da matansu. Abinci aka soma rabawa masu kalangu kuma suka amshe fagen. Haka dai akaci gaba da gudanar da shagalin suna bamu muka tashi ba sai ƙarfe biyun rana. Daga nan kowa ya watse, duk wani gudunmawa a wajen aka bani, sai da muka cika bahun biyu da kaya da atampopi, kuɗi kuwa na same shi sosai ƴan biyu sun yi goshi sosai. Bayan mun koma gida sai na sake wanka na kwalliye da shaddar da Ayashe ta bani na fito shar dani. Sai lokacin na samu nutsuwa naci abinci na ba ƴan biyu nasu abincin. Kafin la'asar har an gama soye naman suna tas Anty Mulka ta ƙuƙƙullama duk waɗanda suka dace, ni dai da Gwadabe cikin ƙaramar samira kawai muka tsira dashi a matsayin rabonmu. Ragon ɗaya sukutum aka ba su Babala, ɗayan kuma ni da ƴan uwana duk muka rataya akai, wanda na samun ma Babala ta aiko laraba wai in ƙara mata nama ƙawayenta na Takai basu samu ba. Dan haushi samirar duka na miƙa mata na yi kwanciyata dan in ɗan huta. Washe gari Ayashe ta ɗau hanyar garinsu, da rana su Sakina suma suka wuce. Uwani dasu Bose ne suka gyara mun ko'ina su kai mun girkin dare kafin magriba duk suka watse ɗakin daga ni sai ƴaƴana misalin taran dare sai ga Gwadabe ya shigo furkarshi ɗauke da fara'a, nima murmushi na sakar mishi. MRS BUKHARI 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundation gidauniyar da muka buɗe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya. Waɗanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE) 300 kacal zasu iya kuɗin karatu NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI INA MIƘA SAƘON GAISUWATA A GAREKU. KHADIJA MAIDOKI MRS BASH MAMANMU (HAJARA ALIYU) MAMAN SAFWAN ANTY YABI YUNUSA JIBRIN ( AZARE) MAMAN ANNUR KHADIJAN MAKAWA UMMU NABEEHA MAMAN YASEER SISTER FARIDA ( ƘAWAR UMMU NABEEHA) MAMAN MUHSEEN RUƘAYYA YAWURI UMMU AFFAN ABUJA UMMU AFFAN SADFAT RAMLEX MMN LAMIDO MAMAN ABDULRAHMAN INNAR BASMA ANTY ZEE MUSA A.A NAFAƊA MAMAN INTEESAR KUNA DA YAWAN DA BAN ISA JEROKU A PEJI ƊAYA BA, A BOYONI BASHI DUK ZAN ZANA SUNAYENKU, INA ALFAHARI DA MASOYANA NA FAƊIN DUNIYA. ( JIYA WATA BEYERABIYA TA KIRANI A WAYA TAKE CEWA DANI TANA BIBIYAR LITTAFINA, KUMA TANA JIN DAƊINSHI SOSAI. SOYAYYAR GWADABE DA IYABO TA BURGETA, KUMA ITAMA HAKA TAKE FUSKANTAR ƘALUBALE A CIKIN AURENTA. ITA KANURI TAKE AURE TANA BEYERABIYA) Lamba ta bakwai (7) Saye nake da doguwar rigar leshi, ɗaya daga cikin kayan da aka bani a gidan aiki. Toye na kwance a kan bargo a ƙasa yana bacci. Ƴan biyu kuma suna kan gado suna baccinsu sun sha overoll farare tas. Yaran ya zuba ma idanu da kyau sai murmushi yake faman yi. Zama yayi a bakin gadon ya ɗauki Taiwo dan tafi kusa dashi. Zama nayi ina fuskantarsu yayi kyau da yarinyar a hannunshi. Rabon yarannan ne yasa iyayenmu suka amince da aurenmu bisa dole, dan wannan rabon ka iya ajalin duk wanda ya kafe ba zamu auri juna ba. Gwadabe ina alfahari da aurenka, ina alfahari da soyayyarka gareni. Hakanne yake sa in mance da kyara, tsangwama, ko ƙyamata daga danginka. Domin kai kam ka zame mun komai, ka cike duk guraben dake da giɓi a rayuwata madallah da samun miji nagari irinka" " Ifemi ( masoyiyata) Na gode da soyayyarki, ina jinjina juriya gami da haƙurinki, samun mace irinki abune da sai an tona shi a wannan zamanin, musamman a ƙabilarku da matan yarbawa suke da zafin rai da saurin faɗa. Mala'ikun Allah ku shaida ni Gwadabe na ɗaga ƙafafuna Iyabo ta shiga aljanna, ku sake shaidawa ita da kishiya sai ta gidan aljanna, a can ma itace shugabar su " Dariya mu ka yi dukkanmu kafin ya ja fasali yace. "Ina da tarin tulin tambayoyi kin shirya?" Ahaf ni dama nasan ba zaka barni ma zuwa gobe ba. Tambayeni in baka amsa, amman kafinnan bari in kawo maka abinci, kana ci kana kora koka kola zai fi. Miƙewa nayi abincin na gefen sib a tiran silver ɗauke da duk abun buƙata. Tuwon shinkafane miyar bushasshen karkashi wacce ta ji kayan cikin rago, iyakar kayan Cikin miyar shine iyakar rabon da muka samu a raguna biyu tiƙa_tiƙa. Zuba mishi nayi na matsar gabanshi, Ajjiye Taiwo yayi tare da sakkowa ƙasa, ya tanƙwashe ƙafarshi yanata kallo ina hidima dashi. Lomar tuwon farko a bakina ya sauke mun, tare da yankan saifa. "Bani labarin tv da kafet tukunna, dan dasu na soma cin karo" Sai da na saisaita nutsuwata, na sake tausasa muryata kafin nace. Burodami Debisi ne ya sake ma Yemisi kayan ɗakinta, shine ya bibbimu da tsofaffin" Kafeshi da idanu nayi ina karantar yanayinshi, dan Gwadabe bashi da daɗi sam ta wajen kishi. Ya zafafa kishinshi sosai akan Burodami Debisi. Alhalin shi babu ni a zuchiyarshi sam, bana mance lokacin da Iyaa tace zata haɗa aurenmu ayi tuwona maina. Har hawaye Burodami Debisi yayi ma iyaa dan ta tausaya mishi ta janye maganar auren. Ba dan ƙiyayya ba sai dai kawai bana daga cikin jerin kalar matan da yake burin rayuwar aure dasu. Ni ina da ƙiba sosai, gani da cikar kumatu dan har idanuna da hancina sun shige ciki, ga mazaunai masha Allah. Shi kuma baya ra'ayin mace mai irin zubina. A cewarshi siriraya doguwar mace yake so, wacce zai iya bi da gudu ta zura ya rufa mata baya. Akan wannan dalilin ya kafe dole cikin fishi da hasala Iyaa ta janye batun aurenmu dole ta ɗauki idanu ta zuba mishi, har kwsnciya jinya ssida yayi. Bayan aurena da shekara biyu ya auri Yemisi ƴar ƙawar Iyaa. "Me yasa daya kawo baki bari na zo kin nuna mun ba?" Kai na sauke ƙasa ganin yanda fuskar Gwadabe ta sauya launi. Ka yi haƙuri in karɓar da nayi ya ɓata maka rai. Amman ba roƙa nayi ba, har gida ya kawo mun. Gwadabe ka rage ƙiyayyar da kake yi ma Burodami Debisi, dan shi ya ɗauki ɗawainiyar rayuwata tun daga yarintata har tasowata. A matsayin wa nake ganinshi, shima bani da wani matsayi a wajenshi daya wuce na ƙanwa" "Ki tsahirta mun haka nan Iyabo. Ai nasan wanki ne, sai dai ai wa ne irin wanda akwai aure a tsakani. Danni na kasa gane menene manufar Debisi sonki yake yi ko tausayinki" Zim naji jikina yayi, ba wannan bane karo na farko da Gwadabe yake ƙumaji sabida debisi ba, kuma ba fa zargina yake yi ba ni na ɗauka a matsayin yana tsare mutuncina da nashi ne baki ɗaya. Gwadabe..." Hannu ya ɗaga ya dakatar dani. Ya soma cin abincinshi zuchiyarshi cunkushe da kishin Debisi har ya gama tsakanin ni dashi babu wanda yayi ko tari, sai ja da sauke numfashi da muke yi. "Batun kuɗin asibiti kuma shima Debisinne ya biya ko, so kike ya samu hujjar ganin kamar bana ƙoƙari a kan ki ko? Bayan kinsan komai da irin tsanar da ake nuna mana. Kina fa gani ƴan uwana ma bana neman taimakonsu" Nasan idanun Gwadabe ya rufe da kishine, shi yasa nayi murmushi nace. Ashe na fika dauriya da haƙuri tunda har na iya haɗa ɗaki da matar da akeson a aura maka. Matar data baro gidan mijjinta sabida kai. Haba Gwadabe in hankali ya gushe hankali ake turawa ya nemo shi. Ko da Burodami ne ya biya kuɗin asibitina bai kamata ace an yi fishi dashi ba, ballema Burodami kokodeen ne ya biya komai da komai." Shiru yayi mun, yasha jinin jikinshi, dan maganata tamkar na ɗaureshi da jijiyoyin jikinshi ne. "Kiyi haƙuri da fishin dana nuna, kishinki ne yai mun yawa. Amman nasan har ga Allah kin fini dauriya da mayar da komai ba komai ba. Mala'ikun Allah ku shaida na sa ma rayuwar Iyabo albarka." Ajjiyar zuchiya na sauke tare da yin dariya. Shima dariyar yayi. "To leshi da kika ɗinka mana shi kuma ta ina kuɗin ya ɓullo?" Labarin yanda akayi na tara kuɗin na bashi tare da kayan kwancen da aka bani a gidan aiki. Miƙewa tsaye nayi na ɗebo mishi duk kayayyakin da na samu na suna, da duk kuɗaɗen da aka babbani. Ka gansu duk albarkar haihuwa ne, kasan ƴan biyu akwaisu da farin jini" Dani dashi mu kaita wauware kayayyakin muna kallo, muna hirarmu ta yaushe gamo, ina bashi labaran abubbuwan da suka faru shima yana bani labarin yanda suka kwashe da Babala kan batun sunan yara da ya saka. Da ankon leshi da muka yi, ashe Babala har kuka saida tayi, wai Gwadabe ya zama beyeraben dole. "Kaya sun yi kyau an gwangwajeki da kaya gaskiya, babu abinda zance sai Allah ya amfana. Sunan yazo mun da sauƙi wallahi ko da yake ance ko wanne yaro da arzikinshi yake tafe" Gaskiya ne kam. Allah ya ƙara rufa mana asirinmu fid duniya wal akira" Gwadabe yace. "Ameen dai Maman ƴan biyu. Toh yanzu me kike ganin ya dace kiyi da kuɗinnan tunda kinga suna da kauri, in yaso sai ki haƙura da zuwa gidan mutane aiki, dama ba asan raina kike zuwa ba, tunda na samu aiki ƙwaƙƙwara a hannuna kema ki miƙe ƙafarki ki huta kamar yadda ko wacce mace take hutawa ko?" Miƙewa nayi na tattare kwanukan daya gama cin abinci na fito falo dasu. Abun mamaki Laila na gani a laɓe tana sauraren hirarmu da Gwadabe. Tana ganin fitowata tayi kamar maiyar da aka kamata ƙiri_ƙiri tana lashe kurwar surukarta, har wayarta tana faɗuwa a ƙasa tsabaragen kaɗuwa. Tsaki nayi mai ƙarfi na harareta. A cikin bahun na zuba kayan wanke_wanken na rufe da bahun na yi komawata ciki. Gwadabe ya sake dawo da maganar sana'a tsabaragen ɓacin rai yasa ban iya ce mishi komai ba, na tuɓe kayan jikina na zura doguwar rigar baccina, nayi hayewata gado na juya bayana ina hawaye." Cikin ɓarin jiki Gwadabe ya hayo gadon yasa hannunshi a kafaɗata, yayi amfani da ƙarfi wajen juyo dani, hawayen da yaga yana tsiyaya ta gefen idanuna ne yasa ya kasa magana. Cikin rishin kuka nace. Yaushene Laila zata bar ɗakinnan Gwadabe ka sanar dani a darennan, wacce hanya ka sama mana ta yanda Laila zata bar gidannan? Ni da ɗakina Laila bata Isa ta hanani zaman lafiya ba, nagaji Gwadabe ni gidanmu zan tafi" Na ƙarashe zancen da rushewa da kuka mai gunji, ji nake yi zuchiyata na yi mun tuƙuƙi. Rungumeni Gwadabe yayi tsam a ƙirjinshi yana rarrashina, amman fur naƙi rarrasuwa. Ana cikin hakane muka jiyo wani ihu daga falo mai razanarwa, wanda yai sanadiyyar farkarmun da yara daga bacci suka saki kuka a tare. Kafin in ɗaukesu muka sake jiyo ihun a karo na biyu. Da sauri Gwadabe ya fita na mara mishi baya da ƴan biyu a hannuna. Me zamu gani hmm Laila muka gani a kwance tana burgima tsaraicinta na fitowa, sai ihu take kwarmayawa. Har ɗan diras ɗinta muna hangowa fari sol dashi, da sauri Gwadabe ya kawar da kanshi gefe. Kafin kace me matan gidan sun cika ɗakin, Laila na ganin haka saita soma kwaɓe suturarta tana fatali da'ita. Ba shiri Gwadabe ya fice a ɗakin. Sai adda'a aketa faman tofeta dashi ita kuma tana ta surutai. Mamanta na ƙurama idanu farare sol dasu luwai_luwai ko wacce mace nayi imani zata so dama itama mamanta haka yake. Kuma Gwadabe fa ya ga maman nata, dan sai da ta yar da rigar maman kafin ya fita har yana tuntuɓe hawayena na share dan nayi imani babu wata iskar dake damun Laila tsagwaron iskanci da makircin data riƙa a matsayin makamin da zai fitar dani daga ɗakina ita ta maye gurbina kenan. Ina tsaye a gefe na kasa daidai da motsawa jiri ne ke shirin zubar dani, da zanyi gigin ɗaga ƙafata tabbas da jiri ne zai kwasheni ya zubar a ƙasa tim. "Sannu Laila Allah ya baku haƙuri. Haula kawo ruwa a bata tasha, ƙilama wani agumun aka mata danta bar gidan a haukace, tunda mu a iyakar saninmu Laila bata da iska." Cewar Yaya Halima wacce take riƙe da kafaɗun Laila. Gude ta ɗauki zani a kujera ta suturta mata ƙirjinta dashi. Ni dai ina tsaye ina kallon bariki. Ruwa aka bata tasha, Babala tace ta kwanta ta rufe idanunta. Ta ko kwanta ta rufe idanta ruf. "Toh Allah shi kyauta, Allah yasa ba mayu bane ma suka kama mata kurwa ba, kunsan jiya an yi taron na ayya" Cewar Babala wacce take hanyar ficewa daga ɗakin. Ina tsaye duk suka watse suka barni, sai muryoyinsu nake jiyowa a ƙofar ɗakina. Rigar maman Laila na bi da idanu kawai na yi ƙuta tare da shigewa ɗaki na kwantar da ƴan biyu da suka koma baccinsu nima na kwanta ina share hawaye mai zafi. A wannan dare Gwadabe ya sha rarrashi sosai, dan birkice mishi nayi kamar lalatacciyar besfa, da ƙyar ya iya shawo kaina a wannan dare. Washe gari muka wayi garin babu walwala sam daga ni har Gwadabe, dan shi kanshi ina ankare dashi da damuwar da tafi tawa ya kwana. Bayan sun dawo daga sallar asuba ya shigo, sai yace "Bari in ɗan kwanta kaina saramun yake yi sosai, zazzaɓi ne ma yake son kamani" Sai jikina yayi sanyi, a tausashe nace dashi. Allah ya ƙara afuwa, sannu inka karya ina da fanadol sai in baka ka haɗiya" Har ya kwanta sai kuma ya tashi, ina shirin ficewa a ɗakin kenan zan juyo ruwan wankan ƴan biyu. "Dawo ki zauna Iyabo mu yi magana " Babu musu ko kafiya a tsakaninmu, cikin saurin bin umarninshi na zauna ina fuuskantarshi. "Wallahi Iyabo ko tsirara Laila zata yi a gabana ba zata taɓa burgeni ba, domin bana daga cikin mazan da suka fifita kyawun mace, ko dirinta. Ni kyawun halinki, da haƙurinki ya fi ye mun komai. Ai mace ta gari farin cikin rayuwar duniya ce. Zance na gaskiya bani da wata hanya da zan bi in kori Laila a ɗakinnan. Ina gudun yawan fishin da Babala take yi a kaina. Dani dake mu yi haƙuri ki taya ni mu yi mata biyayya ta zauna ɗin,in taga dama ta zauna har mahadi ya bayyana, zata ɓata ma kanta lokaci a banza, dan ko matan duniya sun ƙare Gwadabe ba mijin Laila bane. Iyabo na ƴar duma_duma mai hanci a tsakiyar kumata itace nutsuwata. Kiyi haƙuri nasan na danneki da yawa" Shiru nayi kawai ina wani tunani, har ga Allah Ni kam ina yaye Taiwo da Kahinde aurena da Gwadabe yazo ƙarshe ma, nasan ina tafiya babu makawa Laila burinta zai cika na mallakar Gwadabe a matsayin miji. Iyakar son da zan yima Gwadabe kenan in zama tarihi a cikin labarinshi, ko dan ya samu rabauta, dan fishin iyaye bala'ine babba akan yara musamman fishin uwa al'amarin da girma yake" "Baki ce komai ba Iyabo" Ɗagowa nayi muka haɗa idanu nace. Babu komai Gwadabe, zan tayaka biyayya ma Babala ka samu aljanna ta hannunta, Laila taci gaba da zamanta kuma in sha Allah bazan sake asarar hawayena akanta ba. Dukkan wata ƙaddara ko jarabtar da zata samu bawa daga Allah ne, dukkannin wani tsanani baya dauwama face sauƙi ya samu." Ina gama faɗar hakan na miƙe na fita cikin dakiyar zuchiya muka gaggaisa da matan gida suna tsakar gida anata hada_hadar aikin daya zamema mata jiki a rayuwa. Ɗakin Yaya Haula na shiga na durƙusa a gaban Babala na gaisheta, saida nayi baki biyu kafin ta amsamun a yatsine. Yaya Halima kuwa ciki ciki ta amsa, ni banji sautin muryar tata ba ma, sai dai labɓanta da naga sun motsa. Har zan fita Babala tace. "Zo ki zauna Iyabo inason magana dake" Dawowa nayi na zauna kaina a ƙasa ina wasa da gezar majanyin ashoke dana goye Taiwo da Kahinde dukansu a gadon bayana. "Ba komai bane yasa nace kizo ba dama. Kuɗi nake son ki bani kamar dubu talatin haka, inason zan sai taki in tafi dashi, nayi magana da Baban Nazifi hidima tayi mishi yawa, ke kuma naga kin samu kuɗi a wajen suna sosai" To Babala bari in kawo miki" Na miƙe na fita ina jinjina wannan lamari. Nera dubu talatin cib na ƙirgi na kai mata, tako sa hannu ta amshe ba sannu bare madallah. Harna yi ma ƴan biyu wanka na shiryasu ina ta'ajibin wannan al'amari. Toye na ja muka fita tsakar gida nayi mishi wanka a ƙofar ɗaki ya shigo. Ban gusheba sai da na ɗauraye kayan da ƴan biyu suka cire da wanda nasa naci suna, da wanda nasa jiya, dana Gwadabe duka. Kafin in gama wankin matan gidan suka cike igiyoyin da shanya tsab. Sai mayafi na yafa na shiga gidan maƙota na yi shanyata. Ɗaki na shiga na shinfiɗe ƴan biyu a gado, Toye kuma na shafa mishi mai, yasa kaya. Ina juye ruwan wanka na mayar da ruwan kunu kan wutar. Ina fitowa na dama kunu na juye a jug ɗin silver na mayar da ɗumamen tuwon jiya. Ɗaki na shiga na shirya tsab cikin jar atampa sabuwa fil ɗinkin dai buba da zani, yana cikin kayan suna da Iyaa ta hado mun dashi, na murza kwalli da jan baki, na bi jikina da body milk na Mrs Bukhari, na shafa har a ƙasan mamana kunsan masu jego sai da ta'amali da ƙamshi. Ina gyaran falo Gwadabe ya fito daga ɗaki. Murmushi nayi mishi, shima murmushin ya sakar mun. Yallaɓai ka tashi, ya kan naka?" Bai amsa ba sai da ya haɗe jikinshi da nawa, Laila fa duk abinnan tana naɗe a doguwar kujera tana bacci. "Lafiya lau Iyabo, sai kewarki a shinfiɗata. Irin wannan kyau haka Babbar mace kenan, cinyar sa maganin mai haɗama" Dariya muka kwashe dashi kamar babu matsalar dake damun mu. Inason in ji Gwadabe ya kirani da Cinyar sa maganin mai haɗama, ko Babbar mace, daya faɗa sai in jii ƙibata ta sake burgeni, barenma in nai kwalliya, dan kwalliya tafi amsar masu jiki irinmu. To yanzu dai karyawa zaka soma yi ko wanka?" Ido ya kashe mun yace. "To ba sai ki zaɓar mun ba kawai, tunda dai ni mijin Hajiya ne" Ina dariya ciki_ciki nace. To ka soma da wankan, zaka fi jin daɗin karyawar. Ina faɗar haka na fita, har na juye mishi ruwan a bokiti zan je rijiya in sirko, sai ya riƙe hannun bokitin ƙarfen yace. "In banda fitina irin taki kina jego ina ke ina aiki, gafara cus kawai." Ya ɗauki bokitin yayi bakin rijiya dashi. Baban Nazifi dake zaune a turmi yana rage ƙasumbarshi da aska, ya ja tsaki yace. "Allah wadaran naka ya lalace, Laila da majnun ma ƙarshen tarihin soyayyarsu sam babu armashi a ciki. Gwadabe kayi asara shanyayye fitsararre" Ya ci gaba da askinshi, ni kuma na shigewata ciki. Ina haɗa mana abun karyawa a tire mandiya hamshaƙiya ta tashi. Tsaki ta buga, ta fice fuu. Ni kuma na girgiza kai kawai na dure mana abincin a gefe, ni na tattare mata kayan rufarta na sa mata a saman akwatunanta. Na kunna turaren tsinke na Baba flora ɗakin ya biɗe da ƙamshi. Ina zaune ina kallon wani kaset ɗin yarbawa, shiru_shiru yau Gwadabe zai shigo, gobe ne, har goman safe bai shigo ba. Ni kuma yinwa sai sasiƙata take yi, abinci na zuba na soma cin abuna. Ina kan ci wayata na jiyo kukanta daga uwar ɗaki, da sauri na shiga ɗakin. Wata number ne ba suna, ina karawa a kunne na jiyo muryar Gwadabe. "Nine Iyabo. Kiyi haƙuri muna asibiti tare da Babala. Na je dubata na tarar zasu koma asibiti shine muka tafi tare, muna gamawa zan dawo. Kici abincinki kinji? Zan tawo da cefane" To Shikenan Gwadabe Allah ya ƙara mata lafiya, sai kun dawo. Dan Allah ka gaisheta sosai da jikin." "To shikenan Babbar mace zata ji, ki kula mun da kan ki" Mu kai sallama na ajjiye wayar. Ina gama karyawa sai na shige ɗaki har bacci ya soma ɗibata sai naji ana tattaɓani kamar a mafarki naji ana kiran sunana. Ina buɗe idanu naga ashe Uwani ce." Kai Uwani irin wannan duka haka" Na faɗa ina miƙewa zaune. "Ke dai bari Iyabo, damuwace ta ciyo ni shine na kasa haƙuri sai da na tawo. Amman kafinnan akwai abinci a gidan in ɗan sama cikina, tun duku_duku na bar gida babu abunda naci" Ki fita falo zaki ga tire akwai dumamen tuwo da kunu" "Yanzu kuwa zaki ji labari Iyabo in na take cikina" Fita tayi sai gata da tuwo shaƙe da kwano da kununta cikin ƙaton kofi, bayan taci ta yi gyatsa tace. "Tun safe ni da matan gidanmu muka fita muka bazama gari neman aikin yi yinwa na shirin halakamu da yaranmu. Da ƙyar muka samu aiki mu huɗu. Wani sabon asibiti da aka buɗe a bakin titin layinmu to anan ni na samu nawa aikin na wanke bayangidun asibitin, Hafizu kuma Allah ya so shi ya samu gadin get da ƙyar wallahi, a hakanma saida nayi mishi jan ido ya karɓa, gani yake shi yafi ƙarfin gadi, matar gidanmu kuma nata aikin shara da goge gogen ƙasa ne. Iyabo albashin bashi da yawa sam wannan rayuwa ni nama rasa yadda zan tsoma kaina a ciki ga matsalar gidan haya. Shaddarmu fa wata biyu kenan data rufza me gidan yace bazai gyara ba mu da muke haya a gidan mu zamu gyara. To mu bamu ci ba balle har mu iya gyara masai sai dai fa ko wacce mata tayi kashinta a po ta ɗauka taje ta watsa. Gabaki ɗaya gidan sai wari kawai" Jigum nayi ina saurarenta, yinwa bata da daɗi sam ni kaina a baya mun sha kwana da yinwa mu wayi gari babu abinda zamu ci sai ruwa. Uwani rayuwar ta zama sai a hankali, gashi mutane basa son taimako daga ƙwauri sai guiwa kowa nashi ya sani. Amman a ƙalla aikin zai rage muku sosai, sai ku gina rayuwarku akan albashin da kuke ɗauka kusan yanda zaku tsara komai. Allah yasa dai mu dace kawai amman rayuwarma wataran sai kaji duniyar ta fice maka fit a ranka in matsaloli suka haɗu suka cakuɗe maka. Jiya da kinga irin tashin hankalin dana faɗa da daddare da kin tausaya mun sosai" Nan na kwashe labarin iskancin Laila na bata. "Kusun uwa kuma baki yi kukan kura kin dira a wuyanta kin narki shegiya ba?" Kai na girgiza tare da cewa. Hmmm motsi ma wannan na kasa. Ni da nake zaune a ɗofane Uwani ai ina taɓata zata jijjigemun auren nawa ne, kinga burinta ya cika ai ko?" Sai kuma ta sakko tace. "Sai dai dan hakan amman in ba haka ba wallahi da saita gane kuranta. Amman ke haka zaki zuba ido kuci gaba da zama da'ita ko yaya kike so?" Miƙewa nayi tsaye na ɗauki Taiwo na saɓa a baya, na sake sa hannu na ɗauko Kahinde sima na sashi a kusa da ƴar uwarshi, na ɗamaresu tamau da zanin goyo na bisu da majanyi. Hijabina na zura, na saƙa hannu a ƙasan kayana dake jere a wadrop na ciro kudaɗe na soke a giyo. Mu je ki rakani in yo cefane kinji in ɗaura abincin rana, dan Gwadabe suna asibiti da Babala, bansan ko gado za'a kuma basu ba, ko zasu dawo gidaba, ya kamata in gama abinci da wuri" Fita a gidan mu ka yi muna tafe sai tauna matsalolin dake ci mana tuwo a ƙwarya muke ta ta faman yi. A wajen wata beyerabiya mai kayan miya da niƙa na sai tumatiri da albasa da attaruhu, rabi na gyara a wajen na wanke ta niƙa mun, dama mun fito da robar fenti, rabi na ƙunso abina na sayi ɗanyan kifi shawa da su maggi a wajenta, Uwani ma na sai mata haɗin kayan miya na ɗari da hamshin, maggin hamsin, man hamshin, sai kifi ɗanye na hamsin, sai murna da godiya take yi mun. Muna dawowa gida na shiga aikin abinci, ni ina jajjage Uwani na yi mun tsintar shinkafa. Matan gida sai shewa suke yi, ko wacce tana girkinta a ƙofar ɗakinta, Yaya Haula kuwa kajine cikin tukunya take ta aikin musu jar suya gidan ya karaɗe da ƙamshi, Suwaiba kuma kifi take soyawa sukumbiya ɓula_bula, ga jajjage kayan miya tana yi, ga alayyawo ta baje akan tabarma. Kullum su kam a cikin cin daɗi suke kullum baren ma Yaya Haula tunda mijinta kusan shine mai kuɗin familyn baki ɗaya ma. Tukunya na ɗaura na zuba mai na jefa ɓararriyar tafarnuwa guda, man yana yin zafi na zuba jajjagena, na wanke kifina tas na tsaane a kwando, ai sai matan gidan baki ɗaya kallo ya dawo gareni kawai dan hakan sabon abune a tukunyarmu gaskiya, barmu dai da yin fara da mai, ko tuƙa amala da miyar ewodu ko mai babu. Yaya Haula tace. "Lallai bana abun arziki muma ya biyo ta layin gidanmu har mun samu, ayi dai mu gani in tusa zata hura wuta" Sai suka saki shewa dukkansu, ni kuwa ko in kula na gama tsayar da sanwar girkina nasa ma uwani hannu muka ci gaba da tsinta. Sai bayan azahar girkina ya sauka na juye tumaturina a tukunya na mayar kan gawayi. Waya na ɗauka na kira Burodami Debisi nace inason nama na dubu biyu dan Allah ya turo yaro dashi. Bayan mun gama cin abinci sai ko ga yaro da nama cikin ƙaramar baƙar leda dam harda kayan miya cikin leda mai zane, yace kuma in bar kuɗin naman. Allah sarki ɗan uwa mai daɗi kiranshi nayi na dinga yi mishi godiya, ina ajjiye wayar sai ga kiran Gwadabe ashe sun dawo Yana ɗakin Umman Nazifi. Abinci na tafi musu dashi, na gaishe da Babala da jiki, na ɗan jima a ɗakin kafin na fito." MRS BUKHARI 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundation gidauniyar da muka buɗe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya. Waɗanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE) 300 kacal zasu iya kuɗin karatu NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 8 A kwana a tashi A haka rayuwarmu tai ta garawa, yau fari gobe tsumma, babu laifi Alhamdulillah yanzu kam munfi ƙarfin abinda zamu saka a bakin salati. Koda yaushe Gwadabe a cikin tafiye_tafiye yake, duk garin da ya je yakan siyo mana tsarabar garin, su bushasshen kifi, manja, doya, wake, gawayi duk yana siyowa ya kawo. Babala ta jima sosai a gidan sai data warke tsab, ana gobe zanyi arba'in ita kuma ta tattara ta koma ƙauye. Irin ƙoƙarin da taga Gwadabe nayi a kanmu sai ya sake dagula komai. A tsakar gida Babala bata da aikin daya wuce faɗin an ma ɗanta asiri sai wahala nake bashi, ya shiga tarkon yarbawa jikokin oduduwa. In hakan baiyi mata ba sai ta sameni har ɗaki ta ƙaremun tanadi tsab, ni dai zaman gidan gabaki ɗaya ya gundureni, haka naita haƙuri har Allah yasa ta koma Takai. Gwadabe ma haka yasha haƙuri da Babala, damuwa duk ta haɗu tayi mishi yawa, ga matsala da yake samu a wajen ƴan lodi akwai wani bawan Allah da yasa Gwadabe sosai a gaba, domin yawan tashi da motar Gwadabe take yi wajen sufurin kaya, ada yafi kowa ƙwazo a matukan tirelolin har ana mishi kirari da giya dubu, akwaishi da sharara gudu a hanya dandanan sai ya isa ikko, yana isa zai sauke lodi ya sake nauso hanya. To samuwar mota a hannu Gwadabe sai ya doke giya dubu wajen ƙwazo da kazar_kazar bil haƙƙi Gwadabe yake komai. Wata rana ana ma Gwadabe lodi giya dubu shi kuma shigowarshi ƴan lodin kenan, da ya kalli Gwadabe sai yace. "Wata rana ma ba zaka samu ƙafafun da zaka taka mota ba, balle hannayen murza sitoyari in dai muna tasharnan gasa da ni ba daɗi." To daga ni har Gwadabe sai muka shiga damuwa daya dawo yake sanar dani, mu kaita adda'ar neman tsari harda sadaka, ga wannan damuwar ga damuwar Babala abubbuwa suka cakuɗe goma da ashirin. Washe garin ranar da Babala ta tafi muka cika kwanaki arba'in. Ƴan biyu sun yi kuɓul kuɓul dasu gwanin sha'awa. Tun sassafe naketa kaye_kaye dan yau kam a gidanmu zanje in wuni yawon arba'in. Kafin sha biyu na gama duk abinda ya dace, Toye na dawowa daga makaranta, na kwaɓe mishi inifom na watsa mishi ruwa, na shiryashi tsab, naima matan gida sallama. Atampa mai haske nasaka da sabon takalmi da mayafi, ina fita tun kafin in sauka daga kan tudun gidan na soma jiyo hayaniyar muryoyinsu suna gulmar da suka saba. Muna zuwa titi na tari Bus sai ƙofar Nasarawa inda anan gidanmu yake. Cikin layinmu na shiga tun daga titi nake gaggaisawa da mutane, wasu dole ma in tsaya su ga ƴan biyu a haka harna isa ƙofar gidanmu. Gidane mai ɗauke da karamar ƙofa gefe da gefen ƙofar shagunane biyu. Ɗaya na Iyaa Debisi daya na Iyaa Kokodeen. Iyaa Debisi soson danga dasu lagwani, ashana, sitati, gyalu, bula, kayan robibi. Su take siyarwa tana da injin niƙa har biyu dana wuta dana ruwa. A shagonnan mu kai rayuwarmu, akwai ƙofa a cikin shagunan wanda zaka ɓulla babban tsakar gidan namu. Iyaa Kokodeen kuma albo, garin Amala, daddawar kalwa, da bushasshen rogo, garin rogo su take siyarwa harda ma kamun jar dawa. Wannan sana'ar tasu da ita muma mu ka yi wayo muka gansu akai, gashi har yanzu ana takusawa. A bencin dake ƙofar shagon Iyaa Debisi na zauna dan na gaji sosai. Toye kuma yayi cikin gida da gudu. Iyaa Debisi tana zaune a cikin shago taci leshi ɗinkin buba ɗaurin ɗankwalinnan a cukurkuɗe sai gyangyaɗi take ta yi abunta, dama kullum aikinta kenan wannan gyangyaɗi ba'a rabata dashi, kuma a zaune ake yinshi. Iyaa Iyaa!! Na kirayi sunanta tare da ɗan buga benci kaɗan sai ta buɗe idanunta muka haɗa idanu. "Ahhh Iyabo kece da tsakar ranar nan da yara, ku yaran zamani baku da hankali ai mace mai goyo ko ciki bata fitowa sa'ilin da rana ta take. Maza shiga ciki gani nan zuwa. Mahaifiyarki ma yanzu isowarta ko awa ɗaya ba'ayi ba tana ciki" Miƙewa nayi ina fara'a dan na jima banga Mamana ba. Shagon Iyaa Kokodeen na shiga na durƙusa a gabanta na gaisheta , itama tace maza in shiga ciki rana ta take. Ko da na shiga samarin gidan basa nan kowa na wajen aiki, babu ƴan mata a gidan tuni sun jima da aure, Bose ce da aka bari itama gashi tana gidan mijinta. Sai matan ƙannen su Iyaa su su uku Iyaa Beji, da Iyaa Lekan, sai Iyaa Amope. A ɗakinmu na ya da zango mahaifiyata tana tsaye tana sallah goduwa farar bafulata siririya, gata da alkunya da sanyin hali bata iya sakewa tayi hira dani, iyakarta dani gaisuwa da tambayar ya nake ni da mai gidan nawa. Iyakar hirata da'ita kenan saita tsuke bakinta tayi shiru kanta a sunkuye." Tana idarwa ta juyo tace. "Jabu kune a tafe? ( Jabu sunan da dangin mahaifiyata suke kirana dashi kenan, dangin mahaifina kuma iyabo)" Data juyo sai naga ta rame sosai idanunta sun zurma da yawa" Dada kinzo lafiya ina wuni?" Bata amsaba sai miƙo mun hannu da tayi na tashi na sunto yaran na saka mata a cinyarta. Tayi ƙuri tana kallonsu tana musu adda'a. Take Naji hawaye na kwarara a idanuna, Allah ya ɗaura mun tausayinta sosai a zuchiyata. Inna dubeta sai inga kamar tana cikin ƙunci da matsi a gidan aurenta. Dada baki da lafiya ne naga kin rame?" Cikin gurɓatacciyar hausarta ta fulanin daji tace " E jinya nayi kusan wata shida sai dai a kwantar sai dai a tayar, shine dalilin da yasa ban ɓulloku ba." Sai kuma taci gaba da magana dani da yarbanci, dan Hausa mugun wahala take bata, dama da yarbancin muke magana." "Ashe kin samu ƙaruwa Allah ya raya. Ina ɗayan jikan nawa?" Ajjiyar zuchiya na sauke nace. Yana ɗakin Iyaa Beji can na baro shi, ya wajen Baɗɗo da mai gidanta? ( Boɗɗo ƙanwatace a gidan da Dada take aure yanzu, sau ɗaya na taɓa ganinta tal a rayuwata) "Ɓoɗɗo ta haihu tana goyon Daso an yi mun takwara" Sai naji ina kewar ƙannena da dangin mahaifiyata ma, sai naji inason kasancewa dasu. Dada inaso in zaki koma zan tambayi izinin mai gidana zan biki in gano rugarku, inaso lokaci zuwa lokaci in dinga zuwa ziyartarki ke da danginki nima ya kamata yarana su san dangina na wajen uwa su saba" Da sauri ta ɗago ta dubeni tace. "Kar ki soma, kiyi zamanki na yafe miki. Ni zan dinga zuwa ina dubaki kamar yadda na shafe sama da shekaru ashirin ina zuwa ganinki." Ƙur nayi mata da idanu ina karantar yanayinta, duk sai naga ta ruɗe, tashi tayi ta bani su Taiwo ta haye ƙaramin gadon Iyaa ta kwanta ta juya mun baya. Na rasa me ake ɓoye mun ne da Dada bata ƙaunar in ziyarceta, bata son danginta su sanni, to meke faruwa ne tabbas tana ƙasa tana dabo. Iyaa ce ta shigo tana faɗa sosai kamar zata ari baki, tana yi tana dukan cinyarta tanata faman yare. Ashe da Debisi take yi shigowarshi cikin gidan kenan. Da yare yace da'ita. "Kiyi haƙuri Iyaa nifa ba cewa nayi yemisi ta ajjiye aikinta ba, gani nayi ta fifita aikinta fiye da zaman auren da muke yine. Kuma tama ga damar zuwa ta haɗa mun jarfa ne" Ya ƙarashe a sanyaye. Iyaa Kokodeen ce ta shigo ɗakinnan tace. "Haba Iyaa Debisi wannan yaron fa yana da gaskiya kuma ma ai yayi ƙoƙari sosai Ya kamata itama yemisi ta dena zuwa tana yawon kawo ƙararshi wajenki ko wajen mahaifiyarta. Ai ga irinta nan abunda ake hango muku daban abinda kuke hango ma kawunanku daban, ku kun ɗauke mu ba wayayyuba. Dama duk namijin da zai auri soja ai dole sai dai ayi zaman haƙuri." Wannan maganar tamkar ingiza iyaa Debisi Iyaa Kokodeen tayi dama har gobe da mikin ƙin aurena da Burodami Debisi yayi a zuchiyarta. Dan da ƙyar ma aka shawo kanta bayan aurena ta zubar da makaman yaƙinta, macace mai kafiya da binbinni, gata da mita. "Basshi ai duk abinda na guje mishi kenan, shi yasa naso ya auri ƴar uwarshi Iyabo. Musamman dana fahimci ita iyabon tana sonshi. A gida ma ita ke kula da komanshi ina ga ya aurata. Yaronnan ya buɗa mana ƙasa a idanu, dana matsa ya je ya haɗoni da dangin ubanshi akazo aka danneni. To yanzu me yake so ayi mishi? Ai haka zaka je kaita kwashe takaici da baƙin cikin zama da Soja, kuma ban yarda ka sake takurama Yemisi akan batun aikinta ba." Daga ni har Burodami Debisi muka yi tsamo_ tsamo tamkar kazar data faɗa ruwa, ya ɗago mu haɗa idanu ya kasa sabida kunya tare da nadamar abinda ya aikata. Lokacin na shiga tunanowa a zuchiyata, a lokacin da Burodami Debisi ya murtsuke idanunshi yace shi Allah ya kashe shi bazai aureni ba. Ji nayi tamkar alƙiyamatace ta tsaya. Abun bai zo mun da daɗi ba, domin jaririyar zuchiyata da so da tsantsan kaunarshi ta ginu, ban taɓa tunanin zuchiyata zata iya son wani mahaluki bayan Burodami Debisi ba. Ni ban iya sa abu a zuchiyaba, ban iya son abuba. Da wasa da wasa Gwadabe ya maye gurbin dana adana Burodami Debisi a ciki, harya samu matsayin da shi kanshi Burodami Debisi bashi da irinshi. Yanzu kuwa da Gwadabe ya riga ya lasamun giyar sonshi na shiga mayen ƙaunarshi jinshi nake tamkar numfashina, ko kuma bugun zuchiyata, ina ma mijina irin son da har abada bazai iya samun macen da zata so shi kwatan son da nake yi mishi ba. Muryar mahaifiyata ne ya katsemun tunani, cikin ƙwarewa a yaren yarbanci ta soma magana kamar ba bafulatana ba. "Ai aikin gama tuni ya gama. Abinda zai faru ya faru. Jabu tayi aure harda albakar aure. Shima Debisi yayi aure harda ƙaruwar haihuwa. Ni ina ganin Toyosi ki yi haquri ki kawar da wannan batun. Kai kuma Debisi aure ai cike yake da ƙaɗdarori iri daban _daban. Ita kanta Jabu kana ji da ganin irin matsalolin da take fuskanta da dangin mijinta, auren ba daɗinshi take ji ba ana dai zaune zaman yara ko ba haka ba Alima?" Ta kai dubanta kan Iyaa Kokodeen wacce ainihin sunanta Halima, to a harshen yarbanci kuma sukan maiyar da harafin H a matsayin a misali Alima a madadin Halima auwa a madadin Hauwa, Abu a madadin Habu. To itama Iyaa Kokodeen manya da Alima suke kiranta. Ta dubi Dada tace. "Gaskiya ne sosai, mu kanmu wanne haƙurinne ba mu yi ba, namu haƙurinma na mutan da ba irin na yaran zamani ba. " Ranar Burodami yasa mita, sai an kawar da maganar sai can ta dawo da zancan baya. Har Burodami Debisi ya gaji ya bar gidan amman bata sauya zani ba. Haka dai wunina ya kasance bamu muka tashi shirin tafiya gida ba sai da magriba ta kawo kai. Akamu Iyaa Kokodeen ta bani da garin albo dana amala, bata taɓa gajiyawa muddin zanzo sai ta bani. Dada kuma ta miƙo mun ƙunshin bakon da tayo mun tsarabata. Dada yaushe zaki koma, amman zaki zo gidana ko Dada?" Kawar da kai tayi tace. "Me zai kaini gidanki Jabu, ai babu. Jibi zan koma ni kam in sha Allah " To Dada gobe zan dawo akwai saƙo da nake son baki ki ba su Baɗɗo." Kai kawai ta gyaɗa mun. Iyaa kuma ta dire tace ban isa in dawo ba, in Lekan yananan in je ɗakin zaure in kirawoshi in yaso sai ya bini ya amso saƙon" Ba dan naso ba akayi hakan. Da Lekan muka dawo gida. Ƙannena su su huɗu ne, biyu mata biyu maza. Matan na cira musu atampopi guda ɗaɗɗaya sababbi dal. Na cire ma Dada lashi da Atampa coddibuwa, Baffa kuma na cire mishi shadda guda ɗaya ce rak. Na cirama ƙannena mazan kaya kala ɗaɗɗaya a cikin kayan da Hajiya ta bani in ba Gwadabe. Dada na ƙara mata da mayafai da hijabi, da sabon takalmi dan naga takalmin da tazo dashi a ƙafarta takalmin robane duk ya sha liƙi gashi har ɓulewa yayi. Nera dubu goma na zara na miƙa ma Lekan. Yasa hannu kenan zai karɓa Laila ta shigo babu ko sallama. Banji daɗin shigowar tataba sam, bin Lekan da kayan da na soma cusa mishi a bako tayi da kallo. Lekam muje nayi ma bayani a ƙofar gida" Biyoni yayi a tsakar gidanma da idanu yuuu su Yaya Haula suka bini. Baban Nazifi ya daka mun wata tsawa fitowarshi daga ban ɗaki kenan. "Waye wannan sannan wannan kayan da Za'a fita dashi menene a ciki?" Ya jufo mun tambayar bayan ya iso gabanmu. Ɗan fodiyo dake zaune a tabarma suna ƙirga kuɗi shi da Da'u ai sai ya taso yasa hannu ya fisge ledar hannuna ya zazzageta a ƙasa komai suka zubo ƙasa. Ganin matan gidan a gaban kayan Yaya Haula harda salati yasa na fashe da kukan baƙin ciki. Jin amon muryar Yaya Harisu ne yasa na sassauta. "Ina za'a kai kayan. Shi wannan gona_gonan ƙaton da kika shiga ɗakin mijinki dashi alhalin kinsan Gwadaben bayanan fa, ko gwalen naku na yarbawan zaki shigo mana dashi?" Lekan sarkin zuchiya har zai yi magana na dakatar dashi da yarbanci cewar kar ya sake yace komai. Na mayar da hankalina kan Da'u da Baban Nazifi ya bashi umarnin wauwara kayan. Kayan maza da suka gani yasa Baban Nazifi ɗago rigar yace. "Wannan ba rigar Gwadabe bace Iyabo. Wato sace kaya kike yi ƙannenki suna zuwa da daddare suna fitarwa ko? Kenan doguwar rigar Haula data ɓata muna tunanin ruwan sama ne ya gudu da'ita ta rariya ashe kece kika sata? Asirinki ya gama tonuwa a gidannan ƙila harda ƙarshen zamanki " In kada baki in yi magana na kasa. Lekanne yace. "Wannan kayan data samu a sunan Taiwo da Kahinde ne, sauran kuma nata ne na gida, sai kayan mijinta guda biyu. Mahaifiyarta ce tazo daga ƙauye shine ta bayar a kaima ƙannenta, kuna da matsala da hakanne to? Batun sata kuma Antimi Iyabo ba ɓarauniya bace ba'a mana wannan tarbiyyar ba." Salati Gude ta saka tace. "Au ita Iyabon dama tana da ƙanne mu bamu sani ba? Sannan iyakar saninmu uwarta ma ita kanta ba tace ga inda take ba, yasar da'ita tayi tun tana ƙarama ai." Yaya Harisu yace. "To munji babu kayan da zai fita a gidannan. Kai kuma fice mana a gida" Kamar kuwa jira Lekan yake yi ya fita fuu yana sababi da yare. Da manuniya Yaya Haula ta nuna ni tace. "Wabillahillazi huwarrahmanu sai kin biyani doguwar rigata, nera dubu takwas na siyeta , tunda na kama ɓarauniyar rigar." Nan su Gude suka soma tafi tare da yi mun kururuwar naji kunya. Tsugunnawa nayi jikina na rawa na kwashe kayana zan shiga ɗaki dasu, Baban Nazifi ya warce buhun yace. "Har sai kin biya kuɗin rigar da kika sata zaki samu kayanki, Allah wadaran halinki." Tiɓi_tiɓi da kayan mazaunai na tafi ɗaki da gudu na faɗa akan gado na sau rikitaccen kuka irin wanda ban taɓa yin irinshi ba a duniya. A wannan halin Gwadabe ya dawo tafiya ya tarar dani, dan wallahi ko sallamarshi ma banji ba, sai jin hannunshi nayi a jikina, ina ɗagowa da naga shine na kife na sake rugujewa da kuka. A ƙagauce yace. "Wani abunne ya faru da kika je wunin gida ko? Iyabo kiyi haƙuri ki dena kuka akan matsalolinmu dan Allah." Banza nayi mishi da ƙyar ya iya nasarar shawo kaina na faɗa mishi abinda ya faru" Shiru yayi kamar ruwa ya cinyeshi yana riƙe da kumatunshi. Amman naga ranshi ya ɓaci ainun har jijiyoyin goshinshi sun tsaya. "Yanzu kayan suna ina, ina shi Lekan ɗin?" Cikin rawar murya nace. Kayan suna hannun Baban Nazifi, Lekan kuma Yaya Harisu ne ya koreshi." Numfashi ya ja dogo yace. "Ina zuwa ki goya Kahinde da Taiwo zamu fita." Gwadabe na kirayi sunanshi da gaggawa, kulawa ma yabawa dan ko juyowa bai ba. Ina zaune a bakin gado da goyo a bayana, sai na soma jiyo maganganu sama sama ina jiyo tashin muryoyi daga tsakar gida. Ni dai ban ko yi yinƙurin miƙewa ba, hayaniyar sai ƙara tsananta take yi, jin kamar ana titirniyar dambe ne yasa na fito da gudu, aikuwa ƙafafuna suka harɗe na faɗi rib cikina da Manana suka daku da ƙasa. Take wasu hawayen wahala suka wanke mun fuska. Abunka da mai ƙiba sai fa da dabara na miƙe ƙafata naji ta nai mun mugun zafi, a haka na daure na fita. Da'u Gwadabe ya damƙa yake ta kai mishi mahangurɓa, Yaya Harisu na riƙe da Gwadabe ta baya yana jayeshi, Ɗan fodiyo na riƙe da Da'u ga Auwal a tsakiya yayi musu iyaka. Baban Nazifi kuwa yana gefe yana sharce hawaye Yaya Haula tana rarrashinshi kamar wanda jaki ya kada shi da ƙasa. Su kuma matan gidan suna cure waje guda da yaransu maza da mata. "Ni zaka duba ka ce matata ɓarauniyace, me aka kamata ta sata da za a ci zarafinta ita da ɗan uwanta? Kaya kuma ga kuɗin rigarki Haula ku bamu kayanmu" Ban san Gwadabe na da zuchiya haka ba sai yau. Ƴan uwanshi suka rufu a kanshi da zagi da cin zarafina. Baban Nazifi ne ya jefo mana bugun kayan ya sauka a ƙirjina tab, ba da ban ina da ƙiba ba da sai na faɗi. Yaya Haula kuma ta fisge kudin hannun Gwadabe. "Gobe_gobe ku tattare yanaku _yanaku ku bar mun gidana, tunda ba da uwa da uban Iyabo aka haɗa kuɗi akasai gidan ba. Ku kuma ko wacce ta koma ciki ta ja ƴaƴanta" "Kullo ɗakin mu je mu dawo kinji Iyabo?" Ya faɗa yana haki. Da ɗingishi na koma na kullo ɗakin muka fita. Amman fa har muka isa gidanmu babu wanda yace da wani komai. Acanma mun shiga mun samu kab matan gidan da samarin gidan a tsakar gida Iyaa tana ta faman kwakwaso da sababin abinda ya abku. Ai muna shigowa ta dira a wuyan Gwadabe da zagi, har kakan kakanshi sai da ta zaga. Mahaifiyata ta kaɗa kanta ta shige ciki, Gwadabe ya miƙo mun buhun kayan na shiga ɗaki na sameta, na baro Gwadabe na ba iyaa haƙuri amman kamar ƙara ma zigasu yake yi. Ina jiyo sanda Iyaa Kokodeen ta koreshi shima waje. Da ƙyar mahaifiyata ta yarda ta karɓi kayannan, shima sai ajjiyewa nayi a gefenta. Ina gunjin kuka na nufi hanyar waje. Muryarta na rawa tace. "Jabu ki yi ma mijinki biyayya. Muddin shi yana ƙaunarki kar ki sake wannan rikice_rikicen banbanci ƙabila da aketa gwabzawa kice zaki kaso aurenki. Ko beyerabe kika aura ba tsira zaki yi ba. Dan a ƙarƙashin ko wacce igiyar aure akwai ƙalubale, in kika ji na wasu naki ba komai bane. Kice ina gaisheshi bamu samu damar gaisawa ba" Kasa amsata nayi na fice ina dingishi, a ƙofar gida na tad da Gwadabe idanunshi sun rine sosai. Haka muka rankaya gida, a daren dai ɓarawon baccine ya kwashemu muka wayi gari da labarin Baban Nazifi yace dukkansu zasu tafi Takai akwai meeting da za'a gabatar. Ni dai har Gwadabe yai mun sallama ya fita ina sharar hawaye. Ga ƙafata ta aune ta yi him. Tsabar ɓacin rai Gwadabe bai ga ƙafarba bai san ƙafar ta samu rauni ba. Haka na wuni ni dai sukuku ba laka, ƙafa fa kafin la'asar ta sake hayewa da ƙyar nake takawa. Ina zaune akan kujera ina kirɓa sakwara sai ga ƴan Takai sun yi sallama. Gwadabe na ƙura ma idanu sai naga har ya faɗa. Yana isowa ya cafe taɓaryar a ƙoƙarinshi na ganin ya kore damuwar dake cin ranshi. Ya hau dukan sakwara a turmi, dan da nan ya kammala tsab. Durƙusawar da zaiyi ya taya ni kai filas ɗin abinci ciki, sai yaga ƙafata a kumbure. "Me ya samu ƙafarli ta aune haka, kuma kike zaune kina aiki? A'a taso muje maza_maza" Babu shiri muka fice a gidan. "Ɗan iska na mamaji" Cewar Baban Nazifi kenan. Ashe targaɗe naji a idanun sawuna, mai ɗori ya gyara mun muka dawo gida. Bayan sallar isha muna zaune muna cin abinci yke bani labarin yadda akayi a takai. "Abun babu daɗi. Babala dama kinsan sai dai ma ta daɗa kwaye mun baya, gashi Goggo Iyatu tana nan mahaifiyar Laila, itama tai ta kunnawa abun wuta. Mun tsaya akan dukkan abinda ya ɓace a gidannan kece kika sace kuma ni zan biya. Wallahi nayi iyakar yina dan in fahimtar dasu fur sunƙi. Ni dai roƙon da nake yi miki kiyi taka tsantsan kuma ki iya takunki, kisa ma Laila ido sosai, kinsan na faɗa miki ƙasurgumar ɓarauniyace." Kuka na fashe dashi. Kana nufin a haka zanci gaba da zama tare da kai anai mun kallon ɓarauniya, harma duk abinda aka nema aka rasa sai na biya? Gwadabe haƙurina ya ƙare ni na...." "Kul kika bari mala'ilun Allah su yi fishi dake, Allah yayi fishi dake. Iyabo wallahi dukkan wannan abun so akeyi a samu a ukun da da kanmu zamu ji mun haƙura da junanmu, abinda suke so kenan. Nayi duk iya iyawata in kare ki, abun yafi ƙarfinane bazan tsaya ina jayayya da Yaya Hambali ba, domin uba ne, a kafaɗunshi muka girma, Balle kuma Babala da goggo Iyatu. Kiyi haƙuri ni zan dinga biyansu duk abinda suka ce an sace musu." Ya batun korarmu kuma da Baban Nazifi yayi, ba gara mu bar gidan ba, tunda in bana gidan ba mai cewa nayi sata?" Kanshi ya dafe kafin a tausashe yace. "Babala tace ko bayan rants bata yafe ma duk wanda ya bar gidannan ba. Ashe Yaya Hambali da Yaya Harisu sun sai gidajen su Malam Audi, da gidansu Baturiya, wata mai kamawa ma za'a soma aikin fashe katangun a haɗe gidajen. Kinsan bikin Nazifi da Laraba ya ƙarato, nima fa duk yau nake jin labari. Nazifi zai zauna a cikin gidannan da matarshi. Itama Laraban a cikin gidannan zata zauna. Ai kinsan Ilum ɗakin Goggo mai Yaɗiya ko? To shi zata aura, Yaya Hambali zai ɗaukeshi aiki a kasuwa. Ni dai Iyabo abinda nake so dake shine kar ki sake fita tsakar gidannan sai in fita daga gidan zaki yi, ko ban ɗaki zaki shiga. Su girki, wanke_wanke wanki duk kiyi a ɗakinki, kiyi haƙuri damo.." MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Lamba ta tara (9) "Kinga can wajen tudun?" Gwadabe ya nuna mun da hannunshi. Wani dan tudune karami akayishi a falon kamar wajen cin abici. ( Daining )Amman bashi da girma, a wajen na saka kayan kallona. "To ki fito da kayan kallon gobe zan siyo miki teburi da dirowar da zaki dinga zuba kayan abinci a ciki. Zaki dinga amfani da risho, ke ko gawayinne in kika kunna a ƙofar ɗaki daya ruru ki shigo dashi, ki sa labule wajen ya zama miki kicin. Iyabo bana so ki sake fita na kuma na jajjada miki. Kiyi haƙuri wata rana sai labari. Ki daure wallahi ba'a sona haka ke faruwa ba, naso mu bar gidannan muyi nesa da ƴan uwa Kuka babu irin wanda banyi ba, washe gari kuwa sai ga Gwadabe da tebur, da durowarshi gajera ta kicin ɗin ƴan gayu. Tare muka jera kayan tukwanena da ɗan kayan abinci da nake dasu, har randunana a cikin wajen na jera, Gwadabe ya hau ya kafa mun labele, Laila sai zirga_zirga take yi tsakanin tsakar gida da ciki. Bai fita ba sai da ya ciccika mun randunanan da ruwa tab, kana ya fice kasuwa. Ni kuma na shiga aikace, aikacen gidan. Bani na fita tsakar gida ba sai da na gama komai nawa na fito da ruwa bokiti uku na sheƙar a rariya, bokitin dana shake shi da wanki na fita dashi na je maƙota na shanya. Ina dawowa na yi komawata ɗakina. Haka al'amuran rayuwar su kaci gaba da gudana yau fari gobe tsumma. A kwana a tashi, gashi yau mun wayi gari jama'ar Takai suna hanyar shigowa Kano. Gidan namu shaƙe da matan anguwa suna ta faman taya mu aikace_aikacen biki. Dan Yaya Haula hantsice leƙa gidan Kowa, babu gidan da bata shiga, kowa a layinnan ya santa. Gida ya ɗau fenti, ga girma da gidan ya ƙara, sakamakon gidaje biyu na jere damu da Yaya Hambali ya siya, aka rushe katangun gidan ya ƙara girman gaske, kuma yasha gyara sosai. Ɓangaren Amarya Laraba da Ango Nazifi ya sha gyara na musamman. Wajajen la'asar sai ga ƴan Takai sun iso Bus biyu su da gayyar yara raɓe_raɓe, gida ya kacame da hayaniya, amman nifa babu wanda yazo daidai da ƙofar ɗakina . Washe gari aka shiga biki ka'in da na'in. Ranar ɗaurin aure tun duku_ duku muka game jallof ɗin shinkafa, da tuwon shinkafa, harda masa. Su Gwadabe kuma suka kama hanyar Takai dan acan za'a ɗaura auren kasancewar duk haɗin gidane. Ko akwatin Amaryar Nazifi baa'a kaiba, ance in aka kawota sai kawai a miƙa. Akwatuna masu taya suna nan a ɗakin Yaya Haula, ina dai gani matan waje sunata shigowa kallon kaya. Ni ko da nake gidan babu wanda ya neme ni da in zo in ga kaya, nima ban ɗaɗa kaina ba. Bayan azahar maza ƴan ɗaurin aure suka dawo tare da bataliyar maza ƴan Takai. Da yamma lis kuma sai ga jerin gwanon tsofaffi da Amarya an tawo da'iya. Harda Sakina aka tawo, suma sun sha ankonsu na Takai. Muma duk mun ci namu ankon na cikin gida, shaddace mai ruwan toka na iyaye, sai wani yaɗi haka na ƙawayen Amarya dai. A haka taro ya watse, duk da ina kaffa _kaffa sai da Yaya Halima ta ci mun mutunci a cikin mutane, daurewa nayi na shanye dan a ranar ma Takai zasu komai. A dangina babu wanda yai mun kara yazo, Uwani ce dai na matsama bata da yadda zata yi shi yasa tazo. A kwana a tashi asarar mai rai. Wasa wasa ƴan biyu shekararsu guda, har suna dabo, Toye kuma yanata zuwa makaranta. Fitinar gidanmu kuma babu abinda ya ragu sai ƙaruwa, dan sau huɗu Gwadabe na biyan kayan da aka sata. Na huɗun ma har ƙarƙashin kujerata akazo aka saka mun, da suka shigo bincike suka zaro. Nayi imanin Laila ce ta aikata mun hakan ba kowa ba, dan tuggu da munafurci iri iri take haɗawa, tsaraicinta da aljanun ƙarya fa babu abinda laila ta dena, a wannan shekara guda ɗin abubbuwa masu dama sun faru. In baku mance ba nace ina yaye ƴan biyu zan bar gidan, to maganar tana ɗamfare a zuchiyata. Ga zawarawa kullum a cikin sallama da' Laila suke, tare da kawo mata ƙwalam da maƙulashe, amman mayyar tana kan bakarta ita sai Gwadabe. Gwadabe ne yaita bani haƙuri nima ganin na kusan yaye in barshi ma baki ɗaya shi yasa ma ban yi tafiyata ba na haƙura na zauna, na cire damuwar kowa da komai a raina. Kamar wasa wata ranar juma'a sai ga Oga Lurwanu shi da karen motar Gwadabe sun riƙo gwadabe ko iya taka ƙafarshi bayayi, suka shinfiɗe mun shi a doguwar kujera. "Gashi nan kin ganshi, mota ya shiga, amman wallahi sai zaro shi akayi ƙafa taƙi takuwa. Muna kyautata zaton sammu akayi mishi. Dama in dai a raba mutum da kafa ko hannune a harkar tuƙi ba kanshi farau ba. Sai ku dage mishi da maganin gargajiya" Hannu na ɗaura aka ina kuka, shima Gwadabe kukan yake yi yana girgiza mun kai halamar in yi shiru. "Ki gode ma Allah ma, da ba haɗarin mota akasa yayi ba ya ragargaje ba. Dan shima anayi kana tsaka da tuƙi sai kaga zaki ko kura, kana ɗauke hannunka magana ta ƙare. Wasu kuma teku suke gani a gabansu duk sai su dibibice" Ni dai sai mamaki da tsoron sha'anin mutan Duniya duk ya kamani. Nera dubu biyar ya ajjiye mun. "Mu kam zamu koma Gwadabe Allah ya ƙara sauƙi" Su kai mana sallama suka tafi. Kifewa a jikinshi nayi ina kuka kamar fitar rai. "Iyabo ki yi ta mun adda'a Allah zai bani lafiya, ta Allah ba dai ta mutum ba. Ni na ɗauka wannan jarabawace ubangijina ya jarabceni dashi. Bazan ɗaura hakkin akan kowa ba Allah yana madakata yana ji da ganin kowa. Ki yi ta mun adda'a. Kafin in amsa shi Yayyen nashi su kayo sallama suka shigo. Baban Nazifi yace. "Gwadabe haka abun ya faru? Ni ina kasuwa ma shigowata kenan mata suke sanar dani wai an shige da kai a hannu baka tafiya, haɗari ne ya afku kome? Koma dai menene Allah ya kyauta gaba. Ke bamu waje ko?" Ya juyo yana mun kallon tsana, ƴan biyu na kwashe dan kar su damu Babansu. Ina daga uwar ɗaki na kira Iyaa nake sanar mata halin da Gwadabe yake ciki. Halin ko in kula ta nuna, tsaki ma tayi ta kashe wayarta, sai Burodami kokodeen da Burodami Debisi na kira na sanar musu, sai ƙawar arziki Uwani. Su Baban Nazifi sun daɗe sosai a falon kafin daga bisani suka tafi, ni da yaran muka fito. "Iyabo inaso zan ɗaura alwala, gashi ina jin fitsari ma. Zaki iya kuwa?" Murmushi nayi ina hawaye lokaci guda nace. "Ai ko ɗaukarkane kacokam zan iya mijina. Nice a haƙƙu in yi maka duk abinda kake da buƙata" Miƙewa nayi na kai yara uwar ɗaki na kulle, falonma na kulle na tawo da ƙaton po mai murfi, cikin dabara na zamo Gwadabe izuwa kan po ɗinnan. Yayi fitsari na mai tsarki, na sake mayar dashi kan kujera. Daga ni har shi sai muka fashe da kuka na faɗa jikinshi. Allah kenan mai yin yadda yake so da bayinshi. Mutum ya fita da ƙafafuwanshi amman yanzu jibeshi a kwance, abunda yafi ƙarfi yanzu ya fi ƙarfinshi. Su Baban Nazifi daya kamata ace su zasu mai duk wannan amman kowa ya tafi ya barmu. Gwadabe kayi haƙuri kuka ba namu bane fa. Akwai Allah shi zai yi mana sakayya. Ka rungumi ƙaddararks sai Allah ya kawo maka ɗauki. Zaka warke bi izinillahi rabbi" "Iyabo ki duba dangina jinina yanda suka nuna halin ko in kula da abunda ya sameni, babu wanda ya tambayeni ko ina jin wata lalura. Yanzu ko Da'u da ba sai ya zauna ya kula dani ba?"... A'a Gwadabe kar ka ɗaura musu nauyin da ba nasu ba. Ni ya kamaci da in jinyata maka. Karma ka sake tada wannan zancan. Ga bawo kayi alwala." Shi da kanshi yayi alwala ni kuma na wanke mishi ƙafafuwanshi. Gwadabe ka daure in kai ka kan gado kaji, sai kayi zamanka acan. Yanzu nan anjima kaɗan Laila zata tashi kwanciya." "Ba zaki iya kaini ba Iyabo, ki je ki kira Da'u ko Nazifi ɗayansu yazo ya kaini, ko du su biyun." Bana so in mishi musu da To" Na amsa mishi, na fita da po ɗin da yayi fitsari na zubar, sai da na mayar ƙarƙashin gado sannan na je kiran Nazifi da Da'u tare da sanar dasu saƙon dake tafe dani. Abun mamaki ko da suka kinkimeshi su biyun dukkansu sai mitar yayi nauyi suka dinga yi, ƙafarshi ɗaya ma basu kama ba sai janta su kai kii. Ni ko ina durƙushe ina hawaye har suka fice ina kuka. A wajen su Yaya Haula suka shigo suka sameni idanuna sun ƴi luɓu_luɓu dasu. "Ohh ni ƴarnan mutum ba a bakin komai yake ba, yau_ yau ɗinnan Gwadabe ya zama musaki sai an kwantar sai an tayar. Sannu Iyabo kinji sannu" Kalmar musaki data faɗa ya dafani sosai. "Kaimu muje mu yi mishi sannu ko. Laila sai ki kwashe kayanki ki ko ɗakin su Halima da Ƙauwama sai ki koma kinga ƴan zuwa dubiya zasuita sunturi kuma dole falo za'a dinga fito dashi" Ni dai gaba nayi suka biyoni. Suka gama gaisheshi suka fita. Ni kuma ina gefenshi ina tofa mishi adda'a a ƙafar tashi, shi kuma yana kallon silin yayi wani irin sanyi" "Iyabo kinga irin riƙon wulaƙancin da Da'u su kai mun? Kinga yatsan ƙafata ya fashe. Daga kwanciya lalura yau _yau harna soma fuskantar wulaƙanci, sai kace ba ciki ɗaya muke ba. Wannan ƙiyayyar dame tayi kama, ki duba fa yanda su Yaya Hambali suka zo suka dubani wallahi babu damuwar komai a fuskokinsu, sai cewa su kai nima karambanine yasa na shiga sana'ar da bani da ilimi a kanta. Wai sana'ar hatsari gareta." Hawayene suka gangaro daga idanunshi izuwa fuskarshi. Rarrashinshi na dinga yi, a ƙoƙarina na ganin na faranta mishi rai, wala Allah ya samu sassauci. Ruwan ɗumi na zuba a bawon na tsoma tsumma na ɗan gargasa mishi yatsan nashi da yake jini. Ya samu yayi sallah, na bashi abinci a baki da kaina, ina bashi ina sake yi mishi nasihu masu ratsa jiki, akan ya gode Allah ma da ba hatsari yayi yaji raunuka masu yawa ba, da izinin Allah muddin muka dage da adda'a koma sammunne Allah zai bamu nasara, amman zuwa gobe zamu je asibiti. "Babu ko ficika a jikina Iyabo, kuma kinga asibiti sai da kuɗi Iyabo" Haba Gwadabe, zan siyar da atampopina in samu ɗan kuɗin da zamu riƙe a hannunmu, mu gode ma Allah muna da abinda zamu ɗaga mu siyar ma. Ina zuwa da zafi_zafi akan daki ƙarfe. A zabure na miƙe na shiga zaro atamopin sunan ƴan biyu, kala goma na fitar na zuba a bako. Gwadabe bari in je shagon me sai da atampopinnan ta bakin titi yarenmun nan, bazan jima ba, ga yara a falo" Ban tsaya jin abinda zaice ba na fice, sai dai kunsan mutane in suka ganka cikin matsuwa ka fitar da abu zaka siyar, sai su dinga yi maka tayin wulaƙanci. Dubu goma sha biyar ta taya atampopinnan kuma manyan atampopi harda Holland, da ƙyar muka ƙarƙare a sha bakwai da ɗari biyar. A cikin daren yau daga ni har Gwadabe kusan kwana mu kai muna Sallah muna adda'a, wallahi har akai sallar asuba bama ko jin digon bacci sai jarababben ciwon kai daya jarabeni. Ana fitowa Sallah na jiyo sallamar maza a ƙofar ɗakinmu. Baban Nazifi ne yake sanar dani dattawan unguwane suka zo duba Gwadabe. Hijabi nasa kafin nace su shigo. Gaggaisawa mu ka yi dasu, tare da yi mun jajen abinda ya faru, daga bisani kuma suka shiga ciki dubo shi. Ni dai jigum nayi a wajen na rasa me ke yi mun daɗi, a wajen suka fito suka taddani, su kai mun sallama suka fita. Ruwan wanka na juyo a bokiti na shiga da sallamata. Na samu Gwadabe yayi jigum yanata aikin tunani, na sani ban isa na hanashi tunani ba, domin jiya uwar haka da lafiyarshi ras ya fita. Gwadabe bari in ɗan goggoge maka jikinka da tawul sai ka yi asuwaki mu samu mu je asibitin ko?" Sai da ya sauke nannauyar ajjiyar zuchiya yace. "Na yi ma Yaya Hambali magana kan batun asibiti da muke son zuwa. Bai goyi bayan hakan ba, yace ciwon yafi kama da sammu, tunda babu inda yake yi mun ciwo, sai nauyi da ƙafafuna su ka yi, kuma Oga lurwanu ma yace sammu ne" Hakane Gwadabe, amman zuwa asibitin ai yana da amfani, in muka je suka auna basu ga komai ba shikenan sai a yi na gargajiyan "E haka na ce mishi nimaa. Ya dai ce Da'u zai tsaya mu tafi asibitin tare." Goggoge mishi jikinshi nayi tas, na saka shi a po ya rage mararshi, yayi asuwakin zamani, kana na bashi tea da burodi, da ƙyar yaci burodi yanka ɗaya, ni ko iyaka shayin kawai na kurɓa, mu ka jiyo sallamar Uwani. Miƙewa nayi na fita falon ina sharar hawaye, ita kanta uwanin kuka take ta faman yi. Muna cikin haka Da'u da Nazifi suka shigo, basu kula mu ba, ciki suka wuce abinsu. Ni kuma na sallami Toye ya tafi makaranta. Fitowa dashi suka yi, Da'u sai tsaki yake yi. Mu dai bayansu muka bi, ashe sun kira tasi tana tsaye a ƙofar gida. Asibitin Murtala muka wuce, ganin halin da muke ciki sai wani likita yace bari ya bamu gado ayi duk binciken daya dace a tsanake zaifi. Hakan kuwa akayi aka bamu gado a Ward ɗin maza, Da'u da Nazifi kuma jin an riƙe mu a asibiti sai suka yi tafiyarsu. Hawaye kawai nake sharewa, likita yace mu zauna daga waje. "Yanzu tsabaragen ƙiyayya yana ciwon ma ba zasu taimaka mishi ba, a lokacin da yafi buƙatar taimakonsu ba. Tafiya fa suka yi Iyabo" Takaici da damuwa duk suka taru su kai mun yawa sosai. Muna zaune aka fito da Gwadabe a keken da ake tuƙa guragu zasu tafi ayo mishi hoto. "Baiwar Allah ya kamata ace akwai wani namiji da zai tsaya tare da marar lafiyan ba ke mace ba, kinga da su zasu sashi a keke, kuma su tuƙashi zuwa ɗakin hoto. " Nurse ɗin daya tuƙo Gwadabe ne ke magana. Gwadabe na kalla, shima ni yake kallo ya dafe kanshi da hannun dama, idanuwanshi tamkar garwashin wuta. To mun gode, suna hanya masu kula dashi ɗin." Na faɗa mishi haka, kafin ya miƙo mun wata takadda. "Ki je wancan tagar ki biya kuɗin hoto, in mun fito sai ki bari in mun dawo ki bani" Karɓa nayi jikina na rawa, su kuma suka wuce. Kuka na fashe dashi babu ƙaƙƙautawa, Taiwo da Kahinde suna ganin ina kuka suma sai suka soma kukan. "Iyabo kije ki dawo, wannan kukan ya isa haka kinga ga yara suma sun soma. Jakata na kinkima na je na biya kuɗin hoto na dawo. A taƙaice sai da muka wuni zumbur babu wanda yazo daga dangina ko na Gwadabe, Hafizu mijin Uwani ne ya kawo mana abincin da muka ci, da naga magriba na shirin yi na dubi Gwadabe nace. "Inaso zanje gida in dafo ruwan zafi, in tawo da tabarma." A'a su Babala suna hanyar zuwa. Ɗazu da likita ya kiraki Yaya Hambali ya kira ni a waya" Baima gama bayanin ba sai gasu sun iso dukkansu, harda Yaya Haula tana riƙe da filas na ruwan zafi da kular abinci. Da sauri na tashi a kujera na ba Babala waje ta zauna. Abu na farko daya fito daga bakinta shine. "Ba ga irinta ba, akan son gwanance mace kaje ka kai kan ka mahallaka. Waya sani ma ko daga danginta ne aka bugo maka wani agumun. Duk da sammu a tsakanin direbobi abune mai dogon tarihin gaske muma munsan tarihin. Gwadabe bazan yi maka baki ba, amman kaji na rantse maka da girman wanda yayi ni yayi ka buwayi gagara misali. Kana tashi zaka sallami wannan matsiyaciyar ka auri Laila, in ba haka ba sai in tsine maka ka bi duniya uban kowa ya rasa ka. Banga riba a aurenta ba sai ci baya da koma baya da rayuwarka tayi. Ke kuma na dawo kan ki, ki zauna da shirinki, Allah na tasan kafaɗarshi ƙarshen zamanki kenan dashi, ya'isa haka, inason yarona ya dawo yanda yake. Kin shigo cikin zuriyarmu kin tarwatsa mun kan yara." Da kuka taƙarashe zancen, yaranta na bata baki kan ta dena kuka. Baban Nazifi ya ɗaura da cewa. "Ya zame mishi dole ya rabu da'ita matsawar mune danginshi. In kuma zai sake iyaye da ƴan uwane sai mu gani. Sabida wannan baƙar kadarar matar tashi marar asali yasa na kasa tallafama Gwadabe Babala, amman a baya wanne irin so ne banyi mishi ba." Wannan yace wannan, wannan yace wancan kowa sai da ya tofa albarkacin bakinshi. Mu dai mun yi shiru kamar ruwa ya cinyemu. "Babala kima Allah kar ki zama silar rabani da Iyabo, son gaskiya take yi mun, bazan iya samun macen da zata soni rabin nata ba. Iyakar zamana da'ita babu abunda ta taɓa yi mun na assha." Miƙewa Babala tayi tace. "To gaka ga Iyabo. Ta maye maka gurbina dana ƴan uwanka da baka da tamkarsu. Ta zauna tayi jinyarka, ni kuma babu ni babu kai. A cikinku duk wanda ya tsaya ya kula dashi ban yafe mishi ba, ko ya cire dukiyarshi ya ba Gwadabe. Haula ɗauki abincin da kika kawo mu koma dashi. Da gudu nasha gaban Babala ina haki nace. Babala kiyi haƙuri ni nayi miki alƙawarin Gwadabe na warkewa a ranar zan bar gidanshi rabuwa irinta har abada. Bazan iya tafiya in barshi a wannan halin bane, ko babu komai uban Ƴaƴanane, kuma a zamanmu bai taɓa cusgunamun ba. Nima dashi da aurenshi ya fice mun a raina, wallahi ko baki ce ba ya zama dole in rabu da Gwadabe dan ba shi bane autan maza ba, kuma ba mutuwa zanyi ba. Amman fishinki masifa ne, yana buƙatarku yaya Harisu, Babala Gwadabe na buƙatar adda'arki" Duk wannan maganar cikin dimuwa nake yinta. Majinyatan dake kwance, da masu jinyarsu kab hankulansu a kanmu yake. Tsawa Babala ta daka mun. "Gafara dallah. Ke baki da uwa dama da sai in ce ki je kisa ta mai adda'ar mana. Tunda akan ki wannan ciwon ya same shi, ke zaki yi mishi jinya dan ubanki" Fuu suka fita suka barni. Bansan sanda na durƙusa a ƙasan ɗakin ina salati ba, Allah nake ambato a lokacin wani irin duhu ne ke mamaye mun idanuna. Uwani ce ta ɗaga ni. "Tashi Iyabo meye haka kike kuka kamar ƙaramar yarinya, ɗakinnan kab ke suke kallo. Rabuwa da Gwadabe shi ya fiye miki." Jaye ni tayi ta zo ta zaunar dani a kujera. Gwadabe yana kwance idanunshi a buɗe suke amman yayi zurfi a cikin tunani hankalinshi baya tare damu. "Bara in fita bakin asibiti in siyo muku ko da tuwo ne. Zan yi ma Hafizu filashin in ya kirani zan sa ya kawo ruwan zafi." Bani da niyyar bata amsa, itama bata buƙaci amsar tawa ba ta fice. Ƴan biyu suna ƙasa na shinfiɗa musu ɗankwalina suna bacci. Har Uwani taje ta dawo ni da Gwadabe babu wanda ya tanka ɗan uwanshi. Tayi yin duniya muci abinci mun ƙi yarda, damuwar da take gabanmu ta wuci a tsaya ana saka lomar tuwo a baki, ni in banda ɗaci babu abunda bakina yake yi. Mijin Uwani ma yazo yayi roƙon duniya kan mu ci abinci, ni ko magana na kasa, Gwadabe ne ma yake iya cewa a ƙoshe yake. "Iyabo ki taso mu je gidana, in yaso Hafizu zai kwana gobe mu ma dawo" "Ku barta tare dani, ina buƙatarta a kusa dani, damuwar zata yi mun yawa" Cewar Gwadabe, sai lokacin hawaye suka surnano da idanun Gwadabe wasu sirara. Uwani ta tattare yaran su kai mana sallama suka tafi. Da ƙyar ma'aikatan kiwon lafiya suka barni zan yi jinyar Gwadabe kasancewar ward ɗin na maza ne, akwai wata mata itama ita take ma mijinta jinya, sai muka zama mu biyu. Shiru wajen ya ɗauka na kasa rarrashin Gwadabe shima ya kasa rarrashina. Wannan daren na ba makaranta gari ku hasaso da kawunanku. Washe gari sassafe aka sake zuwa aka fita da Gwadabe zuwa wani hoton. Kafin a dawo dashi sai ga Yemisi da Burodami Debisi, da Lekan. Hannunsu riƙe da lodoji. Shigowarsu ke da wuya aka shigo da Gwadabe. Da Burodami Debisi aka kinkimeshi zuwa gado. "Sannu Gwadabe ya jikin, ashe abunda ya faru kenan?" Cewar Burodami Debisi. "Jiki sai godiyar Allah, Iyabo likita yace yana son ganinki" Tashi nayi na nufi ofishin likita. "Duk binciken mu ya tabbatar mana komai nashi lafiya suke. Mun yi hoto har sau biyu bamu ga komai ba. Mun sallameku inaga ku nemi na gargajiya zaifi. Ina mai baku shawarar ku sai mishi keken tuƙa marasa lafiya, yafi muku sauƙi da a dinga kinkimarshi. Ga takaddar sallama, kije ki biya Allah ya ƙara sauƙi" Sai da na share hawayena kana na amshi takaddar bance mishi komai ba na fita. Kuɗin hannuna sai da suka ƙare tas ban tsira da ko ficika ba. Burodami Debisi da Lekan su suka taimakeni wajen ɗaukar Gwadabe muka samu Taxi ta kaimu har ƙofar gida. Baban Nazifi da Yaya Harisu suna tsaye a ƙofar gida su Lekan suka zo suka shige da Gwadabe, na mara musu baya. Tunda muka dawo maƙota sukaita tururuwar shigowa gaishe da Gwadabe, su Iyaa Debisi ma sun tawo kusan dukka gidan, sun kawo abinci da dubu biyar, haka mu kaita karɓar jaje daga mutanen arziki. Babala kuwa a bakin Gude nake jin wai ta koma Takai Laila ma ta je ganin gida. Atampopi na na ɗura a buhu kab harda ma ɗinkakkun bar bari ba, kala huɗu na ware kawai, na ɗauki buhunnan na fita hankali da nutsuwata basa tare dani sam. Siyan wulaƙanci sosai akaima kayan, amman biyan buƙata yafi godon buri, Gwadabe mutum da ɓari ne a wajena. Keken ɗaukar marasa ƙafa ko tsofaffi na siyo ta hannu akan nera dubu ashirin da biyar da ɗari takwas. Ina shigowa gidan kallo ya dawo gareni, ni dai babu wanda na kalla takaina kawai nake yi. Ko Gwadabe yasha ruwan mamakin ganina da wannan wul ciya sosai. Ni dai bance uffanba na tallafeshi na sashi a kan wul ciya ɗinnan. Hawaye ya soma sharewa, ni kuma ina mishi murmushi. "Mala'ikun Allah ku shaida na sama rayuwar Iyabo albarka, kuma na ɗaga mata ƙafafuna domin ta shiga aljanna. Allah yai miki albarka ya kawo mana mafita akan jarabawar da take kanmu" Ameen Gwadabe, ka dena kuka. In sha Allah tunda ina nan kafi ƙarfin zubar da ruwan hawaye." Daga haka muka shiga suntirin bin masu magungunan gargajiya, mu ke nan kullum a tafe, amman babu canji kullum jiya e yau. Tafe tafe sai da mu ka kwashe tsawon wata uku muna abu ɗaya. Dangina da suke ɗan tallafamun suma suka gaji suka watsar. Babala sau biyu kaɗai tazo ta duba Gwadabe, amman ƴan Takai kam sun zazzo sosai. Sakina da Bara'u kam mayar da gidanmu su ka yi kamar aje kasuwa a dawo. Duk wata jigilar zuwa nemo maganin makarin sammun da akaima Gwadabe, tare da Bara'u da Sakina muke zuwa. Abincin da zamu ci Bara'u ke kawo mana. Ayashe da Tamu suma sun mana ƙoƙari sosai. Babbar damuwata ɗaya ce tak har yanzu babu wani sauƙi da aka samu." MRS BUKHARI 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundation gidauniyar da muka buɗe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya. Waɗanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE) 300 kacal zasu iya kuɗin karatu https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAWU ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 10 Duk wannan ƙibar tawa da kuka ji labarinta, wallahi ta zuge sosai, na gama ramewa na fice a hayyacina sosai. Shi kanshi Gwadabe yafi tausayina fiye da kanshi. Bara'u kullum a cikin jinjina ma ƙoƙarina gami da amanaa suke yi. A kullum roƙona shine Allah ya ba Gwadabe lafiya, ya yanke mishi wannan zaman. In zaman cikin ya isheshi shi da kanshi yake tuƙa kekenshi ya fita ƙwar gida ya sha iska. Mun gama siyar da komai namu kuɗin ya ƙare a magani, ɗakina goduwar kujer da kafet kaɗai ya rage, sai tarkacen kwanuka da katifa , itama sabida Gwadabe na barta Wata rana ina zaune ina wankin kayana dana yara sai ga Uwani ta shigo, Gwadabe kuma yana ƙofar gida ya ɗan fita shan iska "Uwar biyu wanki kike yi ne?" Wallahi kuwa, daga ina haka na ganki afujajan?" Na tambayeta tare da kallonta. Sai da ta cire mayafinta kana tace. "Hmm wata harkar arziki na samo Iyabo. Kin ganni daga cikin gari nake gidan Hajiya salamatu, wata matace dake kai ƴan mata da matan aure ƙashashen larabawa ko ƙasashen turawa. Amman kafinnan na samo miki maganin karya sihiri garanti, daga cikin ayayoyin Qur'ani mai girma. Bari in karanto miki, muddin kuka riƙe wannan da izinin Allah kuka yazo ƙarshe a cikin kwana na bakwai Gwadabe zai miƙe da ƙafafuwanshi." Ina jin haka na zabur na saki wanki. Na juyo na zuba mata idanu. Dan Allah faɗi ina saurarenki Uwani" Dariya tayi tace. "Ɗakko biro da takadda ina faɗa miki kina rubutawa, da izinin Allah waraka ta zo." Da sauri ba shiri na yago takadda, na ɗakko fensirin Toye na dawo. "Da farko zaki samu ruwanki mai tsabta. Sai ganyen magarya koraye bushewar inuwa guda bakwai. Sai a karanta suratul fatiha a cikin ruwan da aka zuba magaryan, a dinga karantawa numfashin baki na komawa cikin ruwan Sai a karanta Ayatul kursiyyu ( aya ta 255 na cikin suratul baƙara). Sai a karanta suratul a'afaaf daga kan aya ta 106 zuwa kan aya ta 122. Sai a karanta yunus daga kan aya ta 79 zuwa kan ta 82. Suratul kafirun ƙafa ɗaya. Falaƙi da nasi ƙafa uku_uku Sai a karanta wannan adda'ar. Allahumma rabban nas,azhibil ba'as ashfi wa antash shafila shifa'a illa shifa'uk shafi'un la tugadiru sakaman Ƙafa uku za'a karanta. Sannan za'a iya karawa da wannan adda'ar "Bismillahi urkika min kulli shai'in yu'uziyaks wa min sharri kulli nafsin Allahu yashfiyka, bismillahi urkika Shima ƙafa uku In sha Allah ta'ala idan aka karanta wadannan kuma mutum ya dinga sha sau biyu a rana safe da yamma, yana kuma wanka dashi a waje mai tsabta, ko kokuma a jiƙa tawul a goge jikin marar lafiyan da ruwan maganin. Da izinin Allah cikin sati ɗaya mutum zai warke in dai sihirine a jikinshi. ( Kuma zaku iya jarabawa. Wasu malaman sun ce yana da kyau wanda yake da lafiyarshi ma yayi, domin hakan ka iya zama rigakafi kafi magani kareshi. Wallahu mista'al) Wawuyar ajjiyar zuchiya na sauke tare da yaƙinin sauƙi ya zo ma Gwadabe. Duk da abaya masu magani sun bamu wasu mayuka tare da tofin ayoyin Allah a ciki mun yi amfani dasu da dama. Wasu kuma mu da kanmu muka zubar dasu, dan ganin shirka ta shiga cikin lamarin, amman wannan sai naji na samu nutsuwa dasu ainun. Nagode sosai ƙawata Allah dai ya bar zumunci. Bari ki ga da zafi zafi ake dukan ƙarfe bari in wanko ganyen magaryana, ina da ruwan sama cikin robar fenti sai in yi dashi. Sai fa na gama zan samu nutsuwa." Da sauri na je na ɗebo ganyen magarya adadin na buƙatar na wanko, na kinkimo ruwa da Qur'ani izu shittin. "Af na mance sai an daddaka ganyan magaryar ake zubawa." Cewar Uwani kenan. Da haanzari na ɗauko turmi na daka na zuba a cikin ruwan da bismillahi. Sai da muka kammala na samu nutsuwa har na sauke ajjiyar zuchiya. Daki na kai ruwan maganin na adana kana na fito." "To bani labarin abinda ya kai ki gidan Hajiya Salamatu, uwar shige_shige Uwani" "Wallahi Iyabo ƙasar zan bari zan tafi nemo kuɗi. Amman shekara biyu kawai zan yi in dawo" Zare idanu nayi ina dubanta da mamaki. Ƙasar fa kika ce, to aurenki da yaranki a hannun wa zaki barsu Uwani?" Ajjiyar zuchiya ta sauke tace.."Hafizu zai lura dasu Iyabo. Wannan talauci namu yayi yawa. Duk abinda Hafizu fa ya soma babu albarka sam a ciki. Kuma shi ba jari ba. Ke yanzu haka maganar da nake yi miki ma ina gidanmu fa da yaran. An koremu a gidn haya ko ince miki an watso mana kayanmu tsakiyar layi da ranar Allah. To Hafizun ma shi ya bani shawarar ko zan nemi aikatau na ƙasashe da ake zuwa, ƙanwarshi ma yanzu haka tana Canada a gidan aiki, shima in ya samu tare zamu tafi. Ni fa Iyabo wallahi tafiya zanyi. Su Hajiya ma basu san me ake ciki ba. Babbar damuwar shine ita Hajiya Salamatu tace sai dai in ajjiye dubu Hamsin da kuma ni zan yi ma kaina fasfo. In kuma ba haka ba duk zata yi mun amman zan kai wata shida kafin in gama biyan kuɗin da duk ta kashe mun. In kuma na yi fasfo na ajjiye dubu hamshin, da zaran na tafi a cikin wata biyu zan gama biyan kuɗin girji" Ajjiyar zuchiya na sauke nace. To amman babu wani haɗari a cikin tafiyar dai ko. Kuma ina fatan bata ɓarauniyar hanya za'a tura ku ba Uwani, kuma kin tabbatar Shekara biyun zaki yi ki dawo, kuma zaki iya kare mutuncinki a matsayinki na matar aure, bahaushiya ƴar Najeriya, najeriyarma Arewa?" "To Iyabo ina kyautata zaton hakan. Ke kinga mata aure masu tafiya kuwa? Wallahi sun fi ƴan matan yawa, harda dattijai fa baki gani ba. Kuma ba ta ɓarauniyar hanya zamu bi ba, ta hazo zamu keta " Shiru nayi ina ɗan nazari. Kafin ince da'ita wani abun sai ga Gwadabe ya shigo akan kekenshi. Wannan dalilin yasa dole muka katse hirar tamu. Uwani tai mana sallama ta tafi. Tun daga ranar na soma ba Gwadabe ruwan addu'o'in nan safe da yamma, haka kullum sai na goge mishi jikinshi da ruwan maganin. Allah al Hakim cikin kwana na tara da rana kawai sai ƙafar Gwadabe ta motsa kamar da wasa. "Iyabo ƙafata na motsawa" Na ji ya faɗa cikin zabari. Kafin ma in ƙaraso inda yake harya miƙe tsaye. Suddajar godiya ga mahalicci mu ka yi a tare. Muna ɗagowa Gwadabe ya rungumeni tsam a jikinshi yana shafar bayana, tare da sama rayuwata albarka. "Iyabo kinga ikon Allah ko? Haƙiƙa na sake tsinkewa da lamarin Ubangiji Allah. Allah na gode maka daka bani lafiya. Ya Allah dukkanmin mai ruwa da tsaki akan wannan rashin tafiyar tawa ya Allah ka nuna mishi iyakarshi" Ni kuma sai amsawa da ameen nake yi. Ko yara da suka shigo suka ga Abbansu akan ƙafafunshi sai suka shiga murna harda tsalle. Rungumesu yayi dukkansu. Farin ciki da jin daɗi bazai misaltuba, bazai rubutu ba balle har mai karatu ya fahimta" Bara'u shine mutum na farko daya samu labarin warakar Gwadabe. Ni kuma ta ɓangarena Uwani na soma sanarma, kafin na sanar da gida. Na leƙa tsakar gida duk suna tsakar gidan ko wacce tana aikin girki nace. Ku ta ya mu murna Allah ya ba Gwadabe lafiya, ciwo ya warke" "Warkewa fa kika ce Iyabo?" Cewar Gude, kafin in bata amsa Gwadabe ya fito tsakar gidan. Ai sai suka riƙe bakinsu. "Allah ya bani lafiya haka tace. Gani akan ƙafafuna. Godiya ta tabbata ga Allah" Yana faɗar haka ya koma ciki riƙe da ƴan biyu. A masallaci abun sha'awa Gwadabe yayo sallar magriba, bashi ya shigo gida ba sai bayan isha sabida mutane sun baibayeshi ana mishi barka. Hatta su Baban Nazifi a masallaci suka haɗu da Gwadabe, kamar yadda ya labarta mun sun yi mamakin ganinshi akan ƙafafunshi. Ƙafa mai daɗi yau sai ga Gwadabe a bayan gida yana yin wanka da kanshi, Allah abun godiya ne A daren ranar Gwadabe yasha labarai sosai. Hira mu kai ta zabgawa muna murna da farin ciki. Furucin Babala yananan ɗamfare a zuchiyata ya zame mun ciwo. Na yi alkawarin washe gari zamana a gidan Gwadabe yazo ƙarshe kenan. Har yayi bacci idanuna biyu ina tunanin inda zan nufa in na bar gidan Gwadabe. Wata zuchiyar tace mun. "Ga mahaifiyarki da kike ganin kamar tana da wani ciwo a zuchiyarta me zai hana ki koma hannunta da zama. Tunda yanzu kin mallaki hankalinki?" Idanuna na lumshe wasu siraran hawaye suka gangaro kumatuna. Na jima ina karanta wasiƙar jaki kafin na daure na taso na fito falo na ɗaura alwala na soma Sallah. Bani na tsagaita da sallar ba har sai da naji kiran sallar farko tukunna. Takun fitowar Gwadabe na jiyo. Ƙura ma ƙofar ɗakin idanu nayi. Shine ya fito yana saye da jallabiyya fara. Idanu ya ƙuramun yana sakarmun murmushi me kyau da tsayawa a rai. Take zuchiyata ta sake yin rauni ainun. Ruwan hawaye suka ɓallo daga idanuna zuwa kumatuttukana. Tsugunnowa Gwadabe yayi a gabana, ya shiga share mun hawayen nawa. Abun mamaki ruwan hawayen sam sun ƙi ƙarewa. "Iyabo na yi tunanin hawayen farin cikin ganina akan ƙafafuwana kike yi ai. Amman na fahimci akwai ciwo mai raɗaɗi dake damun ruhinki. Faɗa mun menene matsalar? Naso in kwanta dake daren jiya, ko dan kewar juna da muka yi, amman na rasa gane dalilin da yasa kika kasa bani kan ki, mu raya daren da yake cike dam da farin ciki. Daren da babu daren da zai iya tureshi a ƙwaƙwalenmu" Kuka na fashe dashi mai gunji, na rasa yanda zan yi da raina. Zugi zuchiyata take ta tayi mun. Gwadabe cike ruhina yake dam da farin cikin samun warakarka. Gefen zuchiyata kuma cike da fargabar yanda rayuwata zata koma bayan rabuwarmu. Gwadabe ya zama dole mu rabu, muddin muna son juna so na gaskiya. Mu ɗauka rabuwarmu itama ƙaddarace. Har abada sonka zaita wanzuwa a cikin rayuwata, kullum sake halittar sabo za'ayi. Ta yiwu rabuwarmu ka iya kawo ƙarshen numfashina, ko ya zama silar kamuwa da wani ciwon da zai ta cin naman jikina har sai ya kaini ga kushewa. Amman Gwadabe na sani har duniya ta naɗe ba zaka manta da gudunmawar dana ba rayuwarka ba....." Tashi nayi ina shirin shigewa uwar ɗaki domin soma shirya kayana. Gwadabe kuwa duk illahirin jikinshi rawa kawai yake yi mun. Cikin kaurin murya irin ta cikar mazantaka yace. "Iyabo..." A maimakon in tsaya sai na shige ciki da gudu na saka sakata. A jikin ƙofar na jinjina ina jawo numfashi daga cikin huhuna da ƙyar. Iyabo ki buɗe ƙofarnan dan Allah na roƙe ki kar ki sa zuchiyata ta buga." Ya faɗa hakan a mugun raunace, tsabar ɓarin da jikina yake yi ma na kasa ko da motsawa, jin za'a shiga Masallacine yasa ya fita dole, ina jiyo rufo mana ƙofar falo da yayi. Sai da na haɗa ƴan tsunmokaraina a ƙaramin akwati, na ajjiye gyalena a saman akwatin kafin na tada kabbarar sallah. A lokacin ƴan biyu sun tashi daga bacci. Ina idarwa saina gyara zama na soma azkar, ina yi ina kallon yarana. Toye yana tsakankanin ƴan biyu yana wasa dasu. Sai dariyarsu suke yi. Yara kenan su basu da matsalar komai. Iyaka su yi bacci su tashi su ci abinci. Ku sakko ku je ku yi alwala ku yi salla, na faɗa musu da yaren yarbanci. Dukkansu sai da suka rungumeni kafin na buɗe musu ƙofa suka fita. Ai sai na kife a dadduma na shiga rera wani irin kuka na tashin hankali. Inayin kukan nan ban mance da ambaton Allah ba. Jin hucin mutum nayi a gefe na, Gwadabe ne nasan babu makawa. Riƙo hannuna yayi gam, ya rarrasheni ya kasa, yayi magana wallahi ya kasa. Duk dauriya da irin shanye abu na Gwadabe yau zuchiyarshi a tsinke take. Shima hawayen yake fitarwa a gidanunshi. Mun fi minti goma a haka, yara dai ban sake jiyo ɗuriyarsu ba ma. Sai can Gwadabe yayi ajjiyar zuchiya kana yace. "Iyabo yanzu me kike so in yi, ina alƙawarin da muka ɗaukarma kawunanmu zai kwana, babu rabuwa a tsarin da muka tsaroma rayuwar gidan aurenmu...." Dakata Gwadabe, kar so ya rufe maka idanu, ka kai rayuwarka ga halaka. Wallahi zaman mu babu alkhairi, kuma ba zamu taɓa ganin haske ba. Tunda Babala ko da yaushe a cikin zubar da hawaye take. Ta yiwu bijerema iyayenmu da mu ka yi ne ya jefa mu a cikin halin da muka shisshiga a baya. Siraɗi nawa muka tsallake Gwadabe? Ka tsayar da zuchiyarka kul sona ya ruɗeka, uwa tafi gaban a tsaya ana jayayya da'ita wallahi. Dukkanmu ba zamu so yaranmu su yi mana taurin kan da mu ka yi ma namu iyayen ba, Gwadabe mun zuba taurin kai sosai da sosai. Allah ya jarabcemu da talauci sosai da sosai sakamakon fishin iyaye da muke ciki. Ka daure ka sake ni kawai in tafi" Cikin dashasshiyar murya yace. "Ko dai har yanzu da ragowar soyayyar Debisi a zuchiyarki ne Iyabo? Ni fa bazan iya rayuwa babu ke ba. Da maraici kike so yaranmu su taso ne?" Cikin jin haushi, gami da tausayinshi a haɗe na dubeshi. Nayi mishi uziri dan tabbas a cikin tsaka mai wuyar fita yake, dole nice dai zan lallaɓashi ya sauwaƙe mun. Billa babu ko sofanen son Debisi a zuchiyata. Mutumin daya gujeni sabida halittar ƙibar da Allah ya hore mun, to shin me zan yi dashi a cikin rayuwata. Ka sake ni kawai, domin cika umarnin Babala da cika alkawarin da nayi mata. Ce mata nayi a ranar daka samu lafiya ko kwana da igiyoyin aurenka bana kumawa" Mun fi awa guda muna tataɓurza tsakanina da Gwadabe. Muna cikin haka, Allah da ikonshi muka jiyo sallamar Babala a cikin falo, tana tambayar Toye ko muna ciki ne" Jijjunanmu a mace muka fita falon, ita da Baban Nazifi ne, sai Yaya Harisu. Gurfana nayi a gabansu cikin rawar baki na gaishesu, babu wanda yayi yinƙurin amsawa. "Rana bata ƙarya sai dai uwar ɗiya taji kunya. Gwadabe yau zan yi bacci harda munshari sabida wannan jikar oduduwan zata bar gidannan, igiyoyin aurenka zasu sauka a kanta. Kuma bari kaji danginta ne su kai ma Agumu ( sammu) ba kowa ba, domin ba ƙaunarka suke yi ba. Wajen malamai har biyar muka je, duk maganar ɗaya ce dai. Maza saketa ta kama gabanta yanzu_yanzu. Ko wallahi in tsine maka" Idanuna na runtse bakina, harshena suna kakkarwa kunnena na baza ina jiran kalmar saki. Kamar saukar aradu naji ya furta. "Na sake ta saki ɗaya Babala" Wani wuji_wuji naji yana dibata, take mashashshara ta saukar mun. Ajjiyar zuchiya Babala ta sauke kana tace. "Cikace mata ya zama uku ɗan albarka" Na sake ta saki biyu, in aka haɗa dana baya dana yi uku kenan." Ya faɗa muryarshi a mugun dashe kamar wanda aka shaƙe. Miƙewa nayi tsam, duk da jirin da nake gani, amman bazan iya jure shaaƙar numfashin Gwadabe ba. Uwar ɗaki na shiga, Toye da ƴan biyu suna katifa suna wasansu. Ganina yasa Toye cewa.. "Mama kinga Kahinde yana dukan Taiwo ko, bayan itace yayarshi" Sai da na zari jakata kana nace. Kahinde ka dena dukanta, yayarka ce. Kai kuma Toye ka kula sosai da maraicin ƙannenka. Zan yi wata ƴar tafiyar da bansan yaushe zan dawo ba" Duk da yaron yana da ƙarancin shekaru amman sai naga yayi jigum kamar mai tunani. Kayukansu na shafa tare da saka musu albarka, na fito daga ɗakin a sanyaye, har na kai bakin ƙofar fita na jiyo muryar Babala tana cewa. "Yaran wa kika barma, wa kike tunanin zai riƙe yaran yarbawannan? Maza koma ki kwasosu..." "A'a Babala yara kam zan rayu dasu, ni yafi dacewa in kula dasu tunda dana aurota iyayenta ita gayanta suka bani, kiyi haƙuri dan girman Allah " Gwadabe ya katseta da hanzari. Kai nasa nayi ficewata daga ɗakin. Matan gidan duk suna tsakar gida da yaran gidan, suna hangoni ko wacce ta sau abunda take yi kallo ya koma sama wai shawo ya ɗau giwa. Ni ko murtuke fuskata nayi sosai ta yanda ba wacce zata iya samun fuskar tambayata, nayi ficewata zazzaɓin dake jikina sai tsananta yake yi. Ko da na shiga Bus ɗin unguwarmu na kifa kaina a bayan kujerar dake gabanku ban ɗago ba har sai da muka iso. Duk wannan abun babu ko ɗigon hawayen daya sake zubo mun tunda kunnuwana suka saurari kalmar saki. Ko gidanmu ma bansan ya akayi na iso ba, ganina kawai nayi a ƙofar shagon Iyaa. " Ahh ahhh ahh Iyabo kini o ti sele? ( Me ke faruwa )" Iyaa ta faɗa cikin kwakwazo da kuzuzuta lamarin. Kafin in mata amsa sai ga Iyaa Kokodeen ta fito daga cikin gida, itama ganina ne yasa ta nufo ni. "Iyabo lafiya da sassafe haka harda jaka a hannunki?" Jin haka yasa Iyaa fitowa a kidime zaninta na suɓucewa. "Ahhh ahhh ya sake ta ba? Ai dama mu munsan zaki dawo, ba riƙe aure suke yi ba saki ko da yaushe, da laifi ba laifi saki. Kinga abunda muke guje miki tun ba'aje ko ina ba har ya faru. Da yarenki kika aura da kin samu kwanciyar hankali. Ai sai ki shigo mu ci gaba da zama kafin Allah ya ɓullo miki da wani. In ce dai babu wani ragowar igiyar da tai saura? Dan wallahi kin bar komawa wannan auren, an yi na farko, gana ƙarshe yayi." Duk wannan maganar cikin yare take yi, tana yi tana buga cinya tare da tafa hannaye. Jiyo muryar ta ne ya tilastama su Iyaa Beji fitowa da sauri. Suna fitowa ni kuma na shige cikin shagon Iyaa na ɓulle cikin gida abuna. Ina shiga ɗakin Iyaa na tarar da Yemisi a kwance a ƙaramin gadonmu a kwance da dukkan halamu itama a gida ta kwana. Zama nayi a ƙasa jiɓur. Zaman nawa ke da wuya sai ga su Iyaa sun shigo da duk matan gidan, suka tutsiyeni kan sai na faɗi silar mutuwar auren. Daga masu cewa gwara da aka rabu, sai masu cewa zasu je su ɗebo yaransu su girma a cikin yaren mahaifiyarsu. Ni dai suka sak sani a tsaka mai wuya. "Ki buɗe baki kiyi magana mana kin ma mutane shiru" Babu abunda ya haɗa ni dashi.mahaifiyarshi ce ta bashi umarnin ya sake ni. Igiyoyin auren sun ƙare duka" na faɗa a sanyaye. Da hanzari Yemisi ta tashi zaune zumbur kamar wacce aka tsikara. Idanu muka haɗa, dan na riga na gane manufarta na wannan zabura haka. Iyaa ce ta katse mun kallon Yemisi da nake yi dafe da kirjinta. "Sai da kika gama mishi jinya tas ba, iyayen nashi ba ke suka bari da ɗawainiyarshi ba? Kika kaɗar da kayan ɗakin ki tas komai ya ƙare a nemo lafiyarshi, to ga sakamako kin gani. Wanne irin bijere mana ne baki yi akan Gwadabe ba, amman shi gashi ya nuna miki yafi son uwarshi sama dake" Cewar Iyaa da take magana a tsawace. Iyaa Kokodeen ce tace. "Ahh ki barta haka ta ji da zafi gami da raɗaɗin mutuwar aure, daga baya ayi wacce za'ayi." Da ɗaya da ɗaya suka watse ɗakin ya rage daga Iyaa sai ni da Yemisi. Da ƙyar Yemisi ta amsa gaisuwata har tana hararata. Ni abunda yake damuna shine a gabana da ta kwantar da hankalinta ma ƙila wannan itace gamuwata da'ita ta ƙarshe daga ita har mijinta. Dan a wannan karon garin Kano ta yi mun zafi ainun, na fi son in je rugar mahaifiyata in zauna a cikin danginta da ƙannena nima. Ina cikin zancen zuchi sai ga sallamar Debisi ya shigo. Irin kallon daya watso mun da dukkan halamu Iyaa ta labarta mishi abinda ya faru dani. Kaina a ƙasa na gaisheshi cike da ladabi. "Lafiya lau Iyabo. Sai kuma naji mummunan labari marar daɗin sauraro?" Ɗan murmushi kawai nayi kaina a ƙasa. "To Allah yasa hakan shine a'ala gareku baki ɗaya. Allah ya fito muku da waɗanda za su yi dai dai da rayuwarku. Kar ki saka damuwa a ranki. Shi aure rai gareshi nasan kin sani" Duk wannan maganar da yayi yana tsaye a kaina yake yi. Shigowar Burodami kokodeen, da Anty Mulka, da iyaa, da iyaa Debisi, da duk masu ruwa da tsaki na gidanmu ne yasa Burodami Debisi ya nemi waje ya zauna. Alfa Kulle shine ya shigo a ƙarshe, Wa yake ga mahaifina, ƙani ga Iyaa Debisi cikinsu ɗaya. Kuma ya kasance shine mai ƙarfin faɗe aji a family kasancewar shi kaɗai ne namiji da yai ragowa. Gidanshi yana jikin namu gidan. Amman iyalinshi suna Ibadan da zama, sai dai duk shekara yana kai musu ziyara. Burodami kokodeen ne ya buɗe taron da adda'a kafin Alfa Kulle ya tambayeni cikin yaren yarbanci. "Meye silar rabuwarki da mai gidanki?" Murya na rawa na labarta mishi a taƙaice, sai Iyaa tayi carab tace. "Dama tun auren a difane fa take a gidan auren. Dangin miji kullum cikin ƙyamatarta suke suna aibanta mata yarenmu. Buradomi Kulle meye kai baka zaunar da yarinyar nan ka faɗa mata ba, ba ƙafa tasa tashure ba, sabida ganin ba mu muka tsugunna muka haifeta ba, ƙasa ta rufe ma Toye idanu. Cikinmu nan babu mai son wannan auren " Alfa Kulle yace. "Ta faru ai ta ƙare. Ba shikenan ba auren ya ƙare kan kat ba. Sai. Ki zauna zuwa lokacin da Allah zai ɓullo miki da wani mijin. Inason in koma Rugar mahaifiyata can inda kowanta yake. Dan Allah kar ku hanani wallahi bazan iya zaman Kano ba" Ina jiyo ajjiyar zuchiya da Yemisi ta sauke mai ƙarfi. Iyaa kuma ta dire akan ban fa isa in bar hannunta ba. Sai da kowa dake wajen ya sa baki kafin ta amince sai zubar da hawaye take yi. Burodami Debisi kuwa ya kasa cewa komai. Zahiri bai ji daɗin amince mun da kowa yayi akan komawata ruga ba. "Zuwa yaushe kike son tafiya Iyabo?" Burodami kokodeen ya tambaya. A sanyaye nace. Zuwa gobe in Allah ya kaimu" A haka dai taron ya watse, duk yanda Burodami Debisi yaso keɓancewa dani Matarshi ta hana shi wannan ƙofar. MRS BUKHARI 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundation gidauniyar da muka buɗe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya. Waɗanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE) 300 kacal zasu iya kuɗin karatu https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LAMBA TA SHA ƊAYA (11) *ASSALAMU ALAIKUM MASOYAN IYABO MUNA MIƘA SAƘON GAISUWARMU A GAREKU. IYABO TACE IN SANAR DAKU TANA GODIYA DA KUKA TAYA TA JIN ZAFIN RABUWARTA DA GWADABE. TANA MIƘA ƊUMBUN GAISUWA GAREKU* *(Na sha ƙorafi akan in yi haƙuri inyi har asabar da lahadi. To duba da irin son da kuke nuna ma labarin ƙorafinku ya karɓu a yanzu. Amman da zaran free page ya ƙare zaku dinga samun posting ne daga monday zuwa alhamis kaɗai, juma'a asabar lahadi na hutune. Kuyi mun afuwa kunsan bana wasa da yin posting ina da lalurar idanune shi yasa. Amman zaku samo readmore masu yawa in sha Allah nagode)* Duk yanda Burodami Debisi yaso ni da shi mu samu keɓewa Yemisi ta kulle wannan ƙofar a tsakaninmu. Ta cikin idanunshi nake iya karanto labaran dake cikin zuchiyarshi. A haka na wuni cur a waje ɗaya tamkar mutum mutumi. Maƙotanmu da ƴan uwanmu yarbawa su kai ta shigowa jajanta ma Iyaa. Da ƙyar cikin tursasawa da lallami Burodami Debisi yasa na sa lomar abinci a bakina. Har zuwa wannan lokacin hawaye bai zubo mun ba fa, face ruhina dake gasuwa, haƙiƙa kuka rahamane. Sai dab magriba Burodami Debisi ya shigo hannunshi riƙe da baƙar leda shaƙe da yankakkun kayan marmari ya miƙo mun. Harara matarshi ta watsa mana ta dubemu daga sama har kasa ta buga tsaki. Hannu nasa na amshi ledar nayi godiya ciki_ciki, dan wallahi ko magana akayi mun sai in ji kamar in sa hannu a ka inta kwarmata ihu. Ga mita da Iyaa take ta faman yi da kutuntumama Gwadabe da Babala ashariya. Dan da ƙyar Alfa Kulle ya hanata wai ita sai taje ta ɗebo yara ta dawo dasu. Ni kuma wallahi a wannan lokacin har yaran bana son gani, da duk abinda ya danganci Gwadabe. Iyaa ce ta shigo tai ta ma Yemisi faɗa ita da Burodami ashe saɓani suka samu har ta kai da duk haƙurinshi da kau da kanshi sai da ya ɗaga hannu ya mareta. Ita kuma tana taƙamar soja ce ita shine ta rama, rikicin daya tilasta mata baro gida a daren jiya. Nasiha tayi musu sosai, ya ɗauki matarshi suka koma gida. Fitarsu ke da wuya sai ga uwani da Hajiyarta sun yi sallama idar da sallana kenan ban tashi akan sallayar ba ma, ina jan carbi na amsa sallamarsu. "Hajiya kune da magriba haka a tafe, lamarin Iyabo ya tasoki ko?" Cewar iyaa dake gyara zamanta. Hajiya ta kalleni cikin tausayi tace. "Yanzu sai da aka sako yarinyarnan Toyosi duk irin faɗi tashin da tasha, amman dangin mijinnan nata sai da suka ɗauketa akan yaranta?, jiya Tabalbalin take faɗamun samuwar lafiyar mijin fa." Baki Iyaa ta taɓe tace. "Ai tsuntsun da yaja ruwa shi ruwa kan duka. Ni Hajiya ina murna da mutuwar aurennan, domin in banda wahala babu abunda take sha a wannan gida. Sai da ta game mishi jinya ta sai da komai nata ɗakinta daga robobi sai tukwane fa, shine zai sako mana ita. Ko da yake kiyi haƙuri Hajiya ku Hausawa baku fiye riƙe aure ba" Gaggaisawa mu ka yi, Uwani ta matso inda nake, su Iyaa ma suna hirarsu ta manya. "Yanzu a wanne hali shi Gwadaben yake sai Allah. Nayi imani duk inda yake cike yake da tashin hankali babu mamaki in akace yana gadon asibiti ma. Amman Iyabo me yasa kika baro su Toye? Kinsan fa wuya zasu sha ƙila ma a mayar dasu ƙauye kinga shikenan an kashe musu rayuwa" Inata ƙoƙarin ganin ƙwalla ta zubo a idanuna amman ina, abu yaci tura, idona ya soye. Sai da na sauke ajjiyar zuchiya nace. Gara su yi zamansu a dangin mahaifinsu zai fi. Wuya bata kisa Uwani da wuya na kisa mu yaran yarbawa da tun muna ƙanana zamu dinga mutuwa, ke kinsan irin gwale_gwalen da muka sha. Gobe asubar fari garin zan bari, kinga in na tafi bazan sake waiwayo garin Kano ba, na barta har abada. Kinga zanyi irin tafiyarnan ai bai dace in tafi da yaran mutane ba. In Gwadabe ya ga yaran a kusa dashi a ƙalla zai ji sanyi" Na ƙarashe maganar a raunace. Ƙirji Uwani ta dafe tace. "Ni Uwani Tabalbalin ina zaki koma to iyabo?" Can Adamawa wajen mahaifiyata nake son in je in rayu cikin ƙannena, domin in samu kafaɗar da zan jingina in yi kuka. Ita kanta Dada akwai wata boyayyar damuwa wacce take cin ruhinta ainun, tun tasowata da wannan ƙuncin nake ganinta. Baki ga yanda take ta ramewa ba Uwani" Uwani dai bata so ba, amman babu yanda ta'iya dole haka mu kai sallama. "Iyabo ni ko duk randa na dawo daga Canada, zan zo Iyaa ta bani adireshinki ko a bangon duniya kike zan ziyarceki. Sannan dan Allah ki kwantar da hankalinki ki rungumi ƙaddararki da zaran kin samu mane mi kiyi aurenki kema ko Allah zai sa ki samu nitsuwa." Nagode sosai Allah ya ƙaddara saduwarmu. Kya dinga leƙa yaran in kin samu lokaci." Na sake magana a raunace. Basu suka tafi ba sai wajen taran dare su kai mana sallama bayan sunci Amala. Inayin sallar isha na naɗe a gado bana son ma Iyaa ta cakaleni da faɗa ko hargaginta, fruit ɗin da Burodami ya kaqo mun shi naci. Wajajen goman dare Alfa Kulle ya kawo mun adireshin rugar da mahaifiyata take da inkiyar shi mijin nata da take aure Mahaifin su Baɗɗo. "Tashi ki zauna Iyabo mu tattauna kinga gobe asubar fari ya kamata ki kama hanya dan tafiyarki mai nisan gaske ce. Kece baki sani ba, sanda muka je ƙauyannan kina yarinya ƙarama" Miƙewa nayi daga kwance na zauna kamar yadda ta uwarceni. "To tunda kin nace sai kin koma hannun mahaifiyarki ai shikenan, bazan hana ki ba. Amman fa...." Sai tayi shiru akwai abunda take son sanar dani, amman kuma kamar bata son faɗe ko nauyi yake yi mata ne ni dai ban sani ba. Sai kawai ta ɓige da yi mun nasiha tare da cewa. "Mijin Uwarki ance jarababbene sosai, dan haka sai ki kula kar ki je ki haɗata rigima dashi a wannan gidan yawa, ga kishiyoyi" Ni dai da Toh" kawai nake amsata harta gama na koma na kwanta. Tsawon wannan dare tunanuka ne barkatai sukaita kai komo a ƙwaƙwalwata da tunanin irin rayuwar da zan fuskanta a rugar da mahaifiyata take, da irin karɓar da shi kanshi mijin nata zeyi mini. Gefe ɗaya kuma tunanin Gwadabe da yaran duk ya addabeni, wayata a can gidan na baro mishi abarshi dan bana son damuwa. Washe gari sassafe na kintsa tsab, Iyaa ta ɗan harhaɗa mun tsarabar Kano, da ƴan canjina. Iyaa Kokodeen kuma ta kawo kuɗin mota nera dubu biyar ta ce in ji Burodami kokodeen yace a bani na mota. Matan gida mai ishirin mai hamsin sai aka gagganɗa mun, nayi musu sallama. Ina fita sai ga Burodami Debisi a mashin bespa, hawa nayi ya kaini tashar mota inda na samu motar Adamawa, na ci sa'a ma motar zata shiga har ƙaramar hukumar GIRAI, daga girai in na sauka sai in kuma hawa motar wata rugar kuma, kafin na sake hawa motar asalin rugar da Dada take Tafiya ce bata wasa ba a gabanmu. Dubu biyar Debisi ya bani tare da miƙo mun wata jakar leda. Nagode sosai Allah ya bar zumunci. Allah ya ƙaddara saduwarmu" Idanu ya lumshe yace. "Ki gaishe mun da Dada sosai. Sai na zo in sha Allah " Sallama mu ka yi ya figi besparshi ya fice. Hanyar da yabi na bi da kallo ni kaina bansan tunanin da nake yi ba. Mu biyu ne rak a motar ni da wata bafulatana mai yara biyu, kuma a seat ɗin tsakiyar Bus muke, Bus ɗin babbace sosai mai layi huɗu ce zata ci mutum goma sha huɗu harda direba. Ga motar ragwargwajajjiya ce soai. Mu dai muna zaune jigum. Ita bafulatana ta kusa dani sai wasa take da yaranta suna yara yaren fullanci. Sai lokacin hawaye ya ɓalle mun dana tuno da nawa yaran. Shikenan su da hawa jikina kuma ya ƙare, haka suma zasu taso ba a hannuna ba, kamarr yadda nima na taso ba'a hannun mahaifiyata ba. Suma haka zan haifo musu ƴan uba ko? Kamar yadda Dada ta haifo su Baɗɗo. Kukane sosai ya ciyoni, dole na saka fuskata tsakankanin cinyoyina na yi mai isata ba tare da Bafulatanar kusa dani ta san halin da nake ciki ba. Shigowar wasu fasinjojinne yasa na share hawayena na ɗago. Suma fulaninne amman maza, harda sarƙar fulani mai duwatsu kala kala a wuya da hannunsu, ga gashi sun tara sosai a kawunansu, ga sandunansu da takalmin roba, sai ƙosai da biredi suke ci suna korawa da lemun limca na kwalba. Murmushi ne ya suɓuce mini kawai. Da ɗaya da ɗaya aketa taruwa a cikin motar, kujerar da nake zaune naci sa'a duk mata ne mu huɗu a kujerar, dukkansu da gani fulanin usil ne, gasu da yara a hannu ga goyo raɓe_raɓe, tun kafin motar mu ta tashi suke ta aikin ciye_ciye. Kasancewar sammako duk muka bugo a tashar duk suke takaryawa masu abincin tasha sai ciniki suke zabgawa. Ni ko ko ruwa bana sha'awar sha balle inci abinci, yinwarma da kanta ta hutasshe da tumbina. Sai da rana ta fito ƙal kafin motarmu ta cika tab, nan aka shiga binmu muna biyan kuɗin mota. Dubu ɗaɗɗaya da ɗari biyar kuɗin motar haka muka bayar, waɗanda suke zaune a injin ɗari biyar. Motarmu ta fita daga cikin tasha ta hau lafiyayyen titi. In banda hayaƙi da jijjiga babu abunda motarnan take yi. Ji kake tututu_tuturtu, gashi bata da gudu sam. Kaina na bakin taga ina kallon mutanen dake tafe a ƙasa ɗaiɗaiku. Wasu kasuwannin ƙauye da gani zasu je ciyo kasuwa, yayinda wasu kuma suka fito neman kuɗi, wasu tallace a kansu maza da mata, yara da manya. Tun ina ganin mutane har na soma ganin bishiyoyi. Jama'ar motarmu kuwa sai hirar nishaɗi da jin daɗi suke yi, yayin da wasu suke gyangyaɗi, a yayin wasu suke ciye_ciyensu, wasu kuma suna kame kamar ni haka. Tafiyace miƙaƙƙiya mu kai ta ta faman yinta. Da azahar tayi muka tsaya a wani gidan mai mu kai sallah a masallacin gidan man. Aka firfito kowa na sayen abunda zaici, dan direba yace ba zai sake tsaiwa ba sai mun isa inda zamu sauka. Masu fitsari nayi, masu ba haya nayi. Gurasa da ƙuli na siya na ashirin, na sha ruwa a randar masallaci, nayi komawata cikin mota. Kai mun ɓata lokaci sosai a wannan gidan mai kafin mu ka kama hanya. Mune har bayan la'asar bamu isa ba, sai yamma sakaliya sai gamu a ƙaramar hukumar girei Allah ya iso damu. Ƙauyan abun sha'awa, fulani makiyaya sunata wucewa da garkunan shanayensu zasu koma gida, shanayen manya lafiyayyu gwanin sha'awa, masu tallar nono mata suma sai wucewa suke da ƙoransu a ɗoɗɗore a kawunansu. Sakkowa mu ka yi kowa ƙafafuwa a kumbure. Matar da muka zauna waje guda na tambaya. Baiwar Allah a ina zan samu motar Jere Banyo?" Cikin kwaɓaɓɓiyar hausa tace. "Nima can zani, mu je daga can gaba zamu samu mota sai mu tafi" Ajjiyar zuchiya na sauke, na bi bayanta tiryan_tiryan har zuwa wajen akori kurar dana ga ta cika ta batse da mata da mazan funani. Duk masu tallar nononnan da sukaita wucewa ashe duk can zasu je. Iko sai Allah tafiya mabuɗin ilimi kenan. Haka na haye akori kura na biya nera ɗari, a cakuɗe muke da maza, motar an cika mutane har bana iya shaƙar numfashin kirki, baka jin komai sai warin hammata da ƙarnin nono. Ga hanyar babu kyau, haka mu kaita cuccurewa waje guda da mazan da matan. Na sha ɗan karen wuya ainun kafin mu isa Jere Banyo. A mugun galabaice na fito, ina mayar da numfashina. Masu acaɓa ne naji suna ta ihun faɗin. "Jaɓɓi lamba zaki je, kuzo mu je" A galabaice na isa gaban acaɓar nace. Jaɓɓi lamba zani, nawa ne?" "Nera hamsin ne, hau mu je" Hawa nayi ya ja muka nitsa. Ya Allah birni ma rahamane, kwazazzabo muka dinga shiga, acaɓarnan tana sama tana ƙasa damu tamkar zamu kifa. Ƙarafan acaɓar na riƙe dam, na runtse idandunana inata karanto adda'a,. Ga ƙurar jar bushasshiyar rairayi data cika mun idona da hancina dam. Wallahi na ɗauka kafin in sauka daga acaɓarnan zamu rikito mu afka wani ƙaton ramin, babu kwalta ko guntu. Bani na buɗe idona ba har sai da mai acaɓa yace. "Mun iso madakata fa" kana na buɗe idanuna a hankali na ganni a tashar ƴan acaba. A mugun gajiye na sakko daga acaɓar tare da sallamarshi. Jarabawar dana samu duk yaro ko yarinyar da na tambayeta inane gidan Modibbo Yuguda mai nagge. Sai dai su bini dana mujiya basu iya yaren hausa ba, ni kuma ban iya fullanci ba. Ga duhu ya soma doso kai. Wata baiwar Allah ce ta ja hannuna zuwa gidan wani dattijo. Bayan sun yara yaren fullanci mai daɗi da garɗin saurare sai ya fuskanceni cikin gurɓatacciyar hausa yace. "Gidan Modibbo Yuguda mai nagge kike nema ko yarinya? Dan Ɓingel tace iyakar abunda ta gane a bayaninku kenan" E gidanshi na zo Baba. Ni ƴar wajen matarshi Daso ce, yayar su Ɓodɗo ce daga birnin Kano " Baki ya rike tare da girgiza kanshi, ya dubeni da mamaki maɗaukaki yace. "Kika ce ke ƴar Daso ce kuma daga birnin Kano, to Daso dama tana da wata ƴa?" Take naga ya sauya kala daga fara'a zuwa kicin_kicin. Wata dattijuwar fara sol ɗin bafulatana mai yala yalan gashi ya kirawo ta shiga dani cikin asalin gidan. Bayan yace mun zai tura yanzu a tawo da Dadan. Cikin wata bukka aka shiga dani, sai da na sunkuya sosai kafin na iya shiga cikin bukkar, irin gidajen da suke dashi kenan a rugar . Ban taɓa ganin ɗakin gargajiya a zahirance ba sai yau, ɗakin ya burgeni ya ƙayatar dani. Jeren ƙorene kyawawa masu zanen tsuntsaye da masu zanen ƙadangare gasu nan iri iri an mammanna su a jikin bangon bukkar. Daga kusurwa biyu kuma wasu ƙwaryane hawan hawa a jejjere ko wanne anyi mishi murfo da faifal mai kala_kala. Ɗayar kusurwar kuma jeren kwallane masu hoton tsuntsaye da korayen ciyayi, ga wasu tukwanen ƙasa a kikkife a gefe. Abun al'ajabi baya ƙarewa sai gani ga gadon ƙasa da katifar yayi. Ƙasan cikin bukkar kuma buhune aka ɗinka aka shinfiɗa a matsayin ledar tsakar ɗaki. A gefe na zauna ƙuri ga duhu_ duhu a cikin ɗakin. Wannan dattijuwar ce ta shigo hannunta rike da fitilar aci bal_bal, akwai wani ɗan gini da akayi a saman ɗakin kamar anyi gininne musamman domin ajjiye wannan aci bal_bal ɗin. Bayan ta ajiye sai tace dani. "Use ɓilgel ( sannu yarinya)" Sai naga ta fita. Inaso ince zan yi alwala in yi sallah amman bansan me zance ba, dole haka nayi gum. Can bayan duhu ya mamaye sararin samaniya duniya tayi baƙi ƙirin sai na jiyo muryar Dada. Murya mai zaƙi da siranta, muryar dake raunata zuchiyata take kara mun so da tausayin uwata. Cikin bukkar ta shigo da sallama. Tana saye da wata iriyar jemammiyar atampar dana taɓa sai mata a shekarun baya. Sai ɗan wani yalolon tattararren mayafi mai ruwan ƙwai. Ƙafafuwanta kuwa duk ƙura. Idanu ta ƙura mun ƙur, sai naga guraben idanunta tab da ruwan ƙwalla. "Jabu kece a Jaɓɓi lamba a darennan? Kinsan fa kin tambayeni zaki kawo mana ziyara nace miki a'a. To me yasa zaki yi gaban kanki ki zo, ita kuma uwar taki ta barki bacin tasan...." Sai ta ja bakinta ta tsuƙe tare da sauke gwauron numfashi. "Tawo mu tafi to, kawo jakar in riƙe miki" Ta kai hannunta zata ɗauki jakata nayi wuf na ɗauka. A'a Dada zan ɗauka. Kuma kiyi haƙuri dole ce tasa na zo gareki, dole ce tasa Iyaa ta barni nazo, ba a san ranta na tawo ba" Duk fa maganganunnan da yarbanci muke yinshi. Babu dai abinda tace dani sai naga ta sunkuya ta fice. Bayanta nabi muka fita, muna tafe a jere da juna abinda bamu taɓa yi ba kenan. Tiryan_tiryan mu kaiya tafiya, muna wuce samari da ƴan mata. A yadda na lura kab garin gidajensu iri ɗaya ne, gidajen bukka zagaye da jinka, basu da dangar gini ko da na laka ne. Wani gida muka shiga ƙatoton gaske, mata da yaran gidan nono_nono kowa ya ja zugar abokan hirarshi. Ga aci bal_bal kashi kashi, sai fullanci akeyi ana dariya. Mijin Dada yana zaune akan tabarmar keso da rediyo a gabanshi yana ji, ga abinci da kofi a gabanshi. Sallamar Dada yasa wani yaro namiji da ƴar budurwa suka nufota da sauri suna faɗin. "Use Dada" ( Sannu Dada) Mijinta ya juyo ya dube ni, ya dubi Dada dana fuskanci tun shigowarmu jikinta yake rawa. "Je ki gaishe da Babanku gashi can" Ta dubi wannan ƴar berar da tazo ta tareta sai tai mata yare. Shi kuma namijin sai ya amshi jakar hannuna, ita ƴar budurwar kuma tai mun jagora zuwa wajen mijin Dada, gashi ni ban iya Fullanci ba. Haka dai na durƙusa a gabanshi gaisuwar dai ta kurame mu ka yi, sannan muka zo mu ka tarar da Dada tsaye inda muka barta ta nausa a cikin tunani mai nauyi, har sai da ƴar rakiyata ta jijjiga hannayenta. "Dada am" Tace kafin Dada ta dawo cikin nutsuwarta, bayan ta ja fasali sai ta dubeni tace. "Mu je in kai ki ki gaisa da abokan zamana" Binta nayi a baya ta nuna musu ni, nai musu gaisuwar kurame biyu a cikinsu suna ɗan jin Hausa sai muka gaisa da kyau. Daga cikin ƴan mata da yaran gidan ma suna jin Hausa hakan yasa na ɗan ji sanyi. Amman bansan me Dada tace dasu a kaina ba ni dai. Zungul_zungul na bi bayanta har cikin bukkar da nake da tabbacin nata ɗakun kenan. Babu komai a ɗakin sai tarkace kawai, sai gadon ƙasa da katifar yayi taji zanin gado. A bakin gadon tace in zauna. Bayan na zauna Dada sai ta fita. Wannan budurwar kuma tana wajen tulu tana ɗebo mun ruwa a ƙoƙo, bayan ta bani na sha, sai nace. "Inason zan shiga bayan gida, banyi sallar la'asarba ƙila isha tayi ma ko?" "E muma mun yi sallar Isha. Muje in kai ki" Cikin gurɓatacciyar hausar da ba ko wacce nake ganewa ba tayi maganar. Muna fitowa tsakar gidan sai muka tarar da Dada da abokan zamanta a tabarmar da mijinsu yake zaune. Sai faɗa yake zubowa yana ambaton Daso_Daso. Jikina tuni ya bani a kaina ake tattauna maganganu, da jin ƙarfin muryar kuwa ba magana bace ta daɗi. Na sake gasgata hakanne da na ji muryar Dada na rawa, da kuma irin yanda kab yaran gidan su kai ciko_cirko kuma suka ƙura mun idanu kamar maye yaga jariri. MRS BUKHARI NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Lamba ta sha biyu (12) Da jan ƙafa na bi wannan ƴar budurwar da nake kyautata zaton kanwata ce uwarmu ɗaya. Wani waje ne aka ɗan keɓeshi aka zagaye da kara, nuni taimun da hannunta halamar nanne ban ɗakin. Ruwa ta zuba mun a buta ta miƙo mun nasa hannu na karɓa, tare da shiga ban ɗakin. Ƙasace a ban ɗakin , sai ɗan gefe guda da akayi daɓe inaga a wajen suke wanka, sai ramin shadda a gefe. A ƙyamace nayi bawali na fito, inda zan ɗaura alwala ta nuna mun, naga gidan kamar komai da tsari suke yinshi. Nayi alwala muka fito a tare. Har zuwa wannan lokacin Ina jiyo muryar Dada tana magana. Da ƙyar nayi sallolin da ake bina nayi jigum akan buhun da aka shimfiɗa mun nayi Sallah. Abinci wannan budurwa ta kawo mun a cikin ƙwarya an rufe ƙwaryar da faifai. Ya sunanki ne?" Na tambayeta ina ɗan fara'a. "Sunana Cubu" Kin sanni?" Na sake jefo mata tambaya. Sai ta girgiza mun kanta halamar A'a. Sai na yi ɗan murmushi nace. Ke yarinyar Dada ce?" Sai da tayi dariya sosai kana ta bani amsa ta hanyar ɗaga mun kanta halamar e" Kwaryar abincin na buɗe tuwone da wata miya baƙa ƙirin ba koriya ba, sai wani irin ƙamshin ganye take yi marar daɗi, amman dake ina jin ɗan karen yinwa ba shiri na nutsa hannuna a cikin tuwon. Wallahi da ƙyar na iya haɗiye tuwonnan, ko da na haɗiye dambe mu kai ta tayi, yana shirin dawowa ni kuma ina ƙoƙarin mayar dashi, dan gudun kar suce na ƙyamacesu. Inaga Cubu ta fuskanci bazan iya cin tuwon bane, sai ta miƙe ta kawo mun madarar shanu. Dana kafa kaina sai da na shanye madarar tas. Ina sauke kofin nayi gyatsa, sai ga Dada ta shigo tana sharar hawaye cikin dabara, dan ita a tunaninta ma bamu ganta ba. Zargina ya tabbata akwai wani babban abu da aketa ɓoyemun tsawon shekarunnan da ba'ason ni in sani. Ni kuma ina ganin lokaci yayi daya kamata in sani. Bakin gado ta zauna kanta a ƙasa kamar yadda ta saba tace. "In kin gama cin abincin Cubu ta rakaki gidan Ɓoɗɗo acan zaki kwana, ƙanwatace a gidan itace uwar mijin Baɗɗo uwarmu ɗaya ubanmu ɗaya babu wata matsala. In Allah ya kaimu gobe na dawo tallan nono zan biyo gidan in same ki. Cubu ƙanwarki ce ƙanwar Ɓoɗɗo, yar Yusuf. Amma. Akwai Amaduyal shine a sama da Ɓoɗɗo sai dai shi baya zama, yanzu haka suna togo, sun fita kiwon shanu tsawon shekara biyar basu dawo ba, amman ana jin labarinsu, suna yo aike gida, matarshi Sa'ada tana cikin gidannan, da yaranta biyu" Kai na gyaɗa. mamakin daya kamani shine jin Dada ta ambaci tallan nono, kenan itama tallah take yi kamar yadda na ga wasu guggun mata a Jere Banyo da ƙoren tallarsu? Iko sai Allah ai yaci ace Dada tana zaune ne tana morar haihuwa ba wai ace har yanzu aikin wahala take yi ba. Miƙewa nayi tsaye Cubu ta ɗaukarmun jakar kayana. To sai Allah ya kaimu goben Dada" Na yi magana a mugun sanyaye. Cubu da Yusufu ne suke gaba ina biye dasu a baya, ina kallon gari maza suna kwakkwance a tabarma, wasu kuma sunyi da'ira suna cin abinci. Yayinda samari masu jini a jika suke ta sha'aninsu kawai. Ta wani dandali muka zo wucewa nan naga kyawawan ƴan mata farare, da kyawawan Samari. Ƴan mata na waƙa samari na yi musu tafi. Wasu kuma keɓe suke a gefe guda suna musayar kalaman ƙauna. Rayuwar ƙauye akwai ban ƙawa a cikinta, bugu da ƙari akwai nishaɗi sosai. Tafiyace miƙaƙƙiyar gaske mu kayi kafin mu iso gidan Boɗɗo, duk na gama galabaita, ga gajiyar hanya da dama ban huceta ba, ga wannan tafiya me nisa da muka sake yinta. Suna kwance a tsakar gida mu kai sallama muka shiga, mazan gidan kuma kafin mu shigo sai da mukai musu sallama. Da sauri Boɗɗo ta taso ta tare mu." Ina tsaye bansan me Cubu tace da'ita ba. Kawai sai naga ta rungumeni ta fashe da kuka. "Adda Jabu ashe zan sake ganinki a rayuwa? Cike zukatanmu suke da maraicinki" Ta faɗi hakan da kwaɓaɓɓiyar hausa. Nima hawayene suka gangaro kan kumatuna. Nan Boɗɗo ta shiga dani cikin gida tana ta nunani, ni dai Adda Jabu kawai nake jin tana ambato. Ɗakin Yafendo Kaɓoji ta kaini ƙanwar Dada surukarta kenan. Kanta ta dinga jijjigawa tana nanata sunana. Abunda na fahimta ƙanenane kaɗai sukai farin ciki da ganina. Hannuna Baɗɗo ta jawo muka shiga cikin bukkar data kasance ɗakinta, Su Yusufu na biye damu. Boɗɗo ta kalli su Cubu tace. "Sunanta Adda Jabu. Yayar Amaduyal ce, Dada ce ta haifeta itace yarinyarta ta farko. Ina tunanin sanadintane ke sa Dada ƙunci da zubar hawayen da tun tasowarmu muka tsinci Dada a wannan halin." Runguma suka kawo mun dukkansu ukun, babu nuna ƙyama ba komai. Hawaye masu ɗumi sukaita zurubtu a kumaruna, hankalina a madadin ya kwanta sai ya sake tashi. Ni kaina na jima ina tausayama rayuwar Dada, na daɗe ina zargin bata jin daɗin rayuwa akwai wani babban lamari data ƙunsa a cikin ranta yake nuƙurƙusar rayuwarta. A wannan daren mun yi hira sosai da ƙannena na yaushe gamo, dan su Cubu sunƙi tafiya a cewarsu sai dai du mu kwana a zaune. "Adda Jabu ki ce su tafi, Baffa zai yi faɗa sosai, ko ma yazo gidannan a darennan. Gobe Cubu zata kai nono cikin gari, Yusufu kuma zai fita da Shanu kiyo Kuma zata burga madara ta fitar da man shanu da asuba." Jim na kuma yi jin abinda Boɗɗo take faɗe. Cubu tunda kinsan hakane, ku yi haƙuri ku tafi gida. Ni ina nan na dawo rugarnan kenan, daku zanci gaba da rayuwata" Da kyar na lallaɓasu suka tafi, suna tafiya sai ga mijin Boɗɗo ya shigo ya miƙo balangu a baƙar leda. Boɗɗo ta gabatar mishi dani a matsayin babbar yayarsu. Cike da jin kunya ya sake gaisheni yana sosa ƙeyarshi shi a dole kunyata ce ta kamashi. Kai fulani a kwaisu da kunya da kawaici sosai. Fitar mijin Boɗɗo ke da wuya mu ka jiyo sallamar wata mata da Boɗɗo ta yo kiranta da suna Hama Ƙwarya ta ajjiye mun a gabana tace. "Use baƙuwa" Farar bafulatana doguwa gata da baƙin gashi. Da fara'arta muka gaisa duk da hausar kamar ta yara ƴan koyo suke yinta. "Adda wannan matar wan su Yuguda ce, mijinta shine Babba a gidannan, yana fita aiki cikin birni. Allah sarki, sannu Hama nagode sosai da fura" Murmushi ta kuma yi mun haƙoranta kamar ƙanƙara dan haske, a gaskiya Hama kyakkyawar macece banga wata makusa a tattare da'ita ba face ta rashin wayewa, da ƙazanta kuma dan ƙafarta duk faso fasonnan ya ɗebi wata annakiya ya adana. Ga gashi iya gashi amman kitson a furje kuma cike da yayin katifa. Boɗɗo tace. "Hama wanna itace Babbar yarmu Adda Jabu, ba lallai bane ki san labarinta ba. Nima naci da bin diddigi yasa na san labarinta. Ta taɓa zuwa rugarnan da daɗewa lokacin muna yara ƙananu." Tare da Hama mu ka ci balangunnan mu ka taɓa hira dai haka. Duk da gajiyace ainun a jikina, ga tunane _tunane da suka haɗu suka cukurkuɗe mun rayuwata. Duk wani bugun zuchiyata bugawa yake yi da so da ƙaunar Gwadabe na. Haka tausayin mahaifiyata da son jin matsalarta suma su ka dabaibayeni. Ina fatan in zame mata sanyin idaniya, maganin zubar hawayenta.amman ta yaya tunda mijinta ma bai karɓeni a matsayin ƴa ba, tunda gashi a darennan ya kasa haƙuri ko da kwana guda ne in yi. Ko ma Iyaa Debisi ta faɗa mun yana da faɗa, bauɗaɗɗen mutum ne ainun. Tunani, da zafi, da sauro su suka hanani huce gajiya ta hanyar saka haƙarƙarina a ƙasa, katifar yayin dana kwanta akai sai sossokeni kawai take yi. Babu shiri na miƙe na fito tsakar gidan, duk yawan matan gidan suna kwance a tsakar gida bisa katifun yayi. A kan tabarma na kwanta iska na ɗan hura ni kaɗan. Da haka ɓarawon bacci yayi awon gaba dani izuwa asubar fari, kwaramniya da kukan shanu ne ya farkar dani. Ashe nonon shanu ake ta tatsa, su kuma sai kuka suke yi. Wasu daga cikin matan na gansu suna burga nono da wani itace mai kama da maburgin miyar yauƙi, wasu kuma suna ta aikin dahuwar madarar shanu, yayin da wasu suke sharar garken Shanu, wasu kuma girkin safe suke yi. Ina buɗe idanu Hama dake shara tace. "Jabu kukan nagge ya tashe ki ko? " Tai maganar tana murmushi. Nima Murmushi nayi mata kawai, na miƙe Boɗɗo dake zaune a cikin jerin matan da suke ta burga nono ta miƙo mun buta, tai mun nuni da ban ɗaki. Ruwa na kama na fito na ɗaura alwala na shige ciki. Na jima ina roƙon Allah yayi mun mafita, ya kuma sassauta mun soyayyar Gwadabe a ruhina, bazan roƙi ya cire mun soyayyr ba dan abadan Gwadabe bazai gaza samun gurbi a rayuwata ba. Tunano ƴaƴana yasa hawaye suka zubo mun a kumatuna, ba shiri na miƙe na fita. Ɗaya bayan ɗaya na dinga bin matan gidan muna gaisawa, mun shiga ɗakin ƙanwar Dada ma mun gaisa. Cikin garken shanu Boɗɗo ta jani wai in taya ta mu tatsi nonon Saniya ta dafa mana mu sha. A baya na bita zuwa cikin garken shanun a nan muka tarar da Hama a ciki ita da mijinta suna shafa ma wata saniya magani jikinta duk kuraje ya fito. "Wannan itace baƙuwar tamu Boɗɗo? Ai Hama yanzu take faɗa mun cewar mun yi bakuwa kuma ma ƴar uwa" Cewar mijin Hama wani dogo siririn bafulatani sosai, ga gashi a kwance a kanshi lub, na lura kamar yafi kowa tsayi a gidan, ko dan ya fi kowa sirantane oho. "E Yaya Hamma itace baƙuwar tamu, Ita ce sama da Amaduyal, daga ita sai shi, a birni take aure can Kano" Murmushi ya sake faɗaɗawa yace. "Sannu da zuwa, baki tawo mana da yaran ba?" Ɗan murmusawa nayi bayan mun gaisa nace dashi. Na baro yara a gida sabida makaranta" Baice komai ba sai ɗan murmushi da yayi, ya kaɗa shanu sama da talatin suka bi bayanshi da ƴar sandarshi da halama kiwo zashi. Ni dai ina raɓe a bayan Hama tsoron shanun nake yi, ina dai kallo Boɗɗo na tatso nonon wata farar ƙatuwar saniya mai baƙin ido, ita kuma Hama tana dai ta shafama wannan saniya magani a duk jikinta, kuɗa sai damun saniyar suke yi tana ta kaɗa kanta. Fitowarmu daga cikin garken kenan sai ga su Cubu sun shigo gidan, amman ta wata ƙofa da ban ba ta ƙofar da muka shigo jiya ba. Idanu na ƙura musu, su basu da fari can ɗinnan . Yanda duk suke kallona a kunyace su nai mun kallon so da ƙauna shi yafi komai burgeni sosai. A barandar dake ƙofar bukkar Boɗɗo muka zauna. "Adda Jabu wadannan duk ƙannenki ne iyakarmu mu huɗu ne, shi Amaduyal shi baya nan. Iyakar yaran Dada kenan, nasan baki san iyakarmu ba, kamar yadda suma duka babu wanda ya sanki sai ni, nima saninna gani ɗaya ne." Daɗi ya lulluɓeni ganina a cikin ƴan uwana cikin Dadana, kuma sai kirana suke da Adda Jabu fuskokinsu da zuchiyoyinsu a cike da fara'a. Nawa bazai ma musaltuba. Tuwon farar masara aka kawo mana ɗumame da baƙar miya kamar kwalta, ko miyar meye wannan oho, sai madarar shanu mai zafi, tuwon sai ƙamshin man shanu yake yi. Loma ɗaya da nai karambanin sakawa a bakina da ƙyar da maƙyarƙyata na iya haɗiyewa tare da danneshi da Madara mai ɗumi. Muna zaune a wajen ina ɗan musu tambayoyi suna bani amsa, wata hausar ma da ƙyar suke fahimtar me nake nufi sabida tayi musu girma. A bakinsu naji ai kullum Dada tana zuwa cikin bini kai nono, fura, da man shanu. Tsawon tasowarsu da hakan suka san iyayen nasu, su kuma yara maza kiwon shanu suke fita yi, in suka girma har gari_gari suna iya fita kiwon shanun. Boɗɗo tace. "Ko ni ma kullum ina fita tallar nono, mu da kuɗin wannan nonon muka dogara, bamu da wani abunyi sai kiwo. In mace ta siyar da nono, a ciki zasu ci su sha, su yi sutura, har su tara kuɗin magani in wata saniya ba lafiya a nema mata magani dashi. Ƴan mata kuma da ba aure a kansu, da kuɗin tallar nononsu ake yi musu kayan ɗaki da komai da komai, wata ma har ta tara kuɗi itama ta sai ɗan maraƙi da haka har su zama garken da yaranta zasu ci gado suma. Matan ma a wasu gidajen suna fita kiwo. Ko su Cubu suna zagayawa amman da awaki ba shanu ba." Jigum nayi ina ta kallonsu jikina a mugun mace. Dama duk uba uban tsarabar da Dada take yi mun in zata zo ganina da kuɗin tallar nono take yowa?" Sai naji zubar hawaye masu zafi, tare da saka ɗamarar sauya ma Dada wannan rayuwar tallan da izinin Allah. Ana cikin haka sai muka jiyo sallamar Dada ita da wasu mata su su biyu, sai namiji guda ɗaya sun shigo kai tsaye kasancewar gidan duk dangin junane. Ɗakin Yafendo Kaɓoji suka nufa, mu kuma muka mara musu baya zuwa cikin bukkar. "Zo Jabu ki zauna a kusa da Yafendonki." Wata mai kama da Dada ta faɗa. Kusa daf da ƙafafunta na zauna kaina aƙasa na gaishesu cike da ladabi. Suma cikin karramawa da haba_haba suka amsa. "Wannan ƙannenane duka. Ga Yafendo A'i, ga yafendonki mai sunanki kin zauna a kusa da'ita. Zai Baffanku Musa gashi, sai Yafendonki Kaɓoji gata nan itace surukar Baɗɗo,. Ta nuna mun mahaifiyar mijin Boɗɗo. Kafin ta ɗaura da nuna mun su Cubu tace. " Wadannan kuma duk ƙannenki ne kece babbarsu, Amaduyal baya nan shi kuma na faɗa miki tun jiya." Murmushi kawai nayi dan na lura a damuwa Dada take sosai. Yafendo Jabu ce tace. "Zan ɗaukeki in tafi dake gidana, can ma akwai Daso shekarunku zasu yi ɗaya mijinta rasuwa yayi ya barta da yara tara. Zan zagaya dake dangi su ganki, zaki ɗan jima kafin ki koma ko?" A sanyaye nace. Na dawo nan da zama baki ɗaya ne, auren nawa ya ƙare. Kuma dan Allah a hannun Dada nake son zan zauna" Gabaki ɗaya suka kalleni, banda Dada domin ita bata wani gane Hausa har sai da ƴan uwanta su kai mata tafintar abinda na faɗi. Da sauri ta ɗago ta kafe ni da ido cikin yaren yarbanci tace. "Yanzu sai da wannan auren ya mutu, dangin mahaifinki sun ƙi barinki kiyi zaman auren ko? Dama tun farko da dan tani akabi da Debisin dai zaki aura domin shi yafi cancanta da sanin daraja da kimarki. Ita Iyaan taki ce ta amince miki ki dawo hannuna da zama alhalin tasan komai, zamana tare dake Jabu bazai yiwu ba. Tun jiya da kika shigo garinnan ban runtsaba har zuwa wayewar garin yau. Abinda nake so dake shine ki bi Yafendonki ki zauna a hannunta akwai Daso zaku dinga zuwa tallar nono tare, komai ma zaku ringa yi a tare. Amman ina mai baki shawarar ku koma birni inda kika fi wayo ki ci gaba da zama rayuwar Ruga cike take da ƙalubale, kumama ba iyawa zakiyi ba. Nima in kuɗaɗena suka haɗu zan je in dubo yaran naki. A hannun dangin ubansu kika baro su?" Wasu zafafan hawayene suka gangaro kan kumatuna, tabbas akwai matsala shin mijn Dada baya ƙaunar ganina kenan, baya son ya samu ladan riƙon marainiyar Allah, ko da wani abunne wanda ni ake ta ɓoye mun ne? Duka waɗannan amsoshin na adanasu inaso duk lokacin dana samu lokaci mai kyau da Dada zata amsamun, ta bani tarihin mahaifina cikakke. Dan bansan wasu abubbuwa a game dashi ba sosai. Na dai san sunanshi, sai hotonshi babba dake kafe a falon Iyaa, sai hirarshi da watarana ke shigowa cikinn zance haka in su Iyaa na yi a tsakar gida. Baffa Musa yace. "Allah shi kyauta. Ni ina ganin tabi Jabu ta zaunaa a hannunta ko babu komai zasu dinga ɗebe ma juna kewa ita da Daso. Kuma komai zasu iyayi. Dan in hanuna nace ta komo bani da wata budurwar ƴa a gabana ma. Tunda tace tana son zama a zuba mata ido, in taji wuyar da bata sababa da ƙafafunta zata koma Birni aradu" Yafendo kaɓoji tace. "A barta a hannuna tana ganin Boɗɗo sai hankalinta ya kwanta, kuma anan akwai Hama naga tun jiya da tazo suke hirarsu tare, kuma akwai matan ƙannenta a cikin gidan ƙila tafi jin daɗi. Kema Adda Daso zuwa ganinta zai fi miki sauƙi. Zasu dinga zuwa tallar nono da Hama dan kar damuwa ta dameta." Baffa Musa yace. "A'a ki barta dai Jabu ta tafi da'ita can wajen nata. Ita kanta Daso tana buƙatar wacce zasu dinga shawartawa dan gudun damuwa. Ke Jabu ki je ki ɗebo kayanki sai ku tafi, Allah bashi in ita Daso mahaifiyarki ta samu daidaito da Mijinta kya dawo hannun nata, duk da nasan mutumme bauɗaɗɗe ga taurin kai da dagiya. A kan ki meye ba'ayiba a shekarun baya da suka shuɗe. Ita yar mahaifinkiToyosi ai tasan komai yaƙi an yishi" Bani da zaɓi dole haka na kinkimi jakata na bi Yafendona zuwa gidanta, tafiya mu ka yi mai ɗa karen nisa, kamar ma ba ƙauye ɗaya suke da Dada ba, kuma fa a ƙafa su kamar ma basa son hawa Acaɓa. Gidanta kam ita kaɗaice a yadda na lura daga ita sai mijinta da yaranta. "Jabu ga ɗakin Daso ki shiga ki ajjiye jakarki, zan tafi tallar nono yanzu, ki shirya sai in kai ki wajen Daso ku zauna kina tayata miƙa Nono. Mu nan ba'a zama daga masu kiwo sai masu fita tallar Nono " Ɗan murmushi na ƙaƙaro kawai. Bukkar data nuna mun ciki na shiga na ajjiye kayana a gefen gadon ƙasa, a kusa da inda naga jakar kayan da nake zaton na mai ɗakin ce Daso. Taya Yafendo ɗaukar ƙwaryar nono ɗaya da buhun bakonta nayi. Muna tafe muna cin karo da mata da yara kowa da ƙwaryarshi ta nono a ka za'a tafi talla. Maza da samari kuma sai wuce mu da garke_garken shanu suke yi suna shiga jeji kiwo. Rayuwar ƙauyen ta matuƙar bani sha'awa, gasu da tsabta ainun kamar ba ƴan ƙauye ba ma, ƴan ƙazaman basu da yawa. Wannan akori kurar muka kuma shiga cike da mata masu tallar Nono, sai yarata yaren Fulani suke ta faman yi, ni dai ina cikinsu ƙwalam har muka iso babban titin mota inda matafiya ke wucewa, anan naga mata da yara jejjere a titi sai ƙulla Nono a leda suke yi, wasu kuma suna damawa. "Mu je kinga ga can Daso bari in kai ki wajenta, ni cikin gari can nake zuwa tallan nono ni da Daso uwarki" Zungui_zungui na bita har gaban wata siririyar fara sol ɗin mace kamanninta kamar an tsaga kara ita da Dadarmu, har kaminnin ya ɓaci. A cikin yaranta ma babu wadda yayi kamannin da ita irin haka. Dariya Yafendo tayi ganin irin yadda na ƙure Daso da ido. "Daso kenan mai kama da Adda Daso sak. Sanadiyyar kamanninsu ne yasa taci sunanta. Daso ga ƴar uwarki tazo daga birni . Zata taya ki siyar da Nono, in yaso zuwa gobe itama sai ta fito da nata ƙwaryar." Hannuna Daso ta jawo ta matso dani kusa daf da'ita. Sai farin cikin ganina take yi kamar dama can ta sanni. Da Yafendona ta yarata mata wacece ni da yare ai sai ta rungumeni tana mai cike da farin ciki. Nima sai naji zuchiyata ta ɗan yi wasai. Anan Yafendo ta sake hawa abun hawa ita da tawagar wasu mata. Mu kuma duk motar da tazo wucewa sai mu tawo da gudu ana turereniya a tsakani, yayinda kowa ke son asai nashi. Haka suke yin tallarsu. A gefen titin cikin ciyawa mu kai sallar azahar, Daso ta dama mun fura da nono da siga cikin ƙoƙo. Tas na shanye furarnan ga nonon ba tsami sai garɗi. Wajajen bayan la'asar lis muka ɗau hanyar komawa gida, nono da furar da Daso ta ɗauko ya ƙare duka. Ko da muka doso ƙofar gidan sai mu ka ci karo da Yaya Hamma mijin Hama a tsaye a ƙofar gidan hannunshi riƙe da ƴar baƙar ledarshi. Yana ganinmu yayi murmushi. "Yaya Hamma kaine a tafe da yamma sakaliya haka?" Cewar Daso kenan. "Nine Daso, kin ganni na jima ina sallama ashe babu kowa ne a gidan? Jabu har dake baƙuwa aka je tallan Nono, har kin huce gajiyar tafiya kenan?" Kaina na sauke ƙasa ina wasa da zoben azurfar da Gwadabe ya sai mun lokacin muna nema. In ma na zauna Ni kadai a gidan, ba daɗi zanji ba, tunanine kawai zai addabeni. Amman kaga dana shiga cikin mata ƴan uwana sai na ji daɗi." Shiru yayi baice komai ba. Daso tace. "Yaya Hamma mu shiga daga ciki mu zauna ai hirar zata fi daɗi ko?" Bai mata musu ba, ya kutsa kai cikin gidan muka mara mishi baya muma. Kano Gwadabe:. Tun bayan fitar Iyabo daga ɗakinta bayan Babala ta tursasa yayi sakin. Hawaye suka zubo daga guraben idanuwanshi. Yana jin wani zafi da turirin zuchiyarshi, ji yake tamkar rayuwarshi ce aka tsayar mishi. Maganar Yaya Hambali ne ya dawo dashi cikin hayyacinshi. "Shikenan ɗan uwanmu ya dawo mana, kai yau zan zuba ruwa a ƙasa in sha. Babala ni sabida jin daɗin wannan sakin ko? Zan buɗe ma Gwadabe katafaren shagon kayan masarufi, uwar kuɗince kawai tawa amman dangane da riba ko ta miliyan zai samu babu ruwana da kuɗinshi." Murmushi Babala tayi tace. "Ato yanzu ne shi kanshi zai dawo cikin hayyacinshi daya rabu da ala ƙaƙai. Kasan Allah duk abunda Gwadabe yake yi ba'a cikin hayyacinshi yake ba sam yarinyar ta game dabaibayeshi da asiri baya ganin kowa da gashi. To ta faru ta ƙare, ni naso ma ta tafi da yaranta da zai fi, dan babu wanda zai ƙaunacesu, kuma bazan bari Laila tayi wahalar yarannan ba wallahi." Yaya Hambali yace. "Yanzu ma ai sai dai ki tafi dasu ƙauye Babala kafin yayi wani auren sai a dawo ma da Laila su, ki dai yi haƙuri Lailan ta riƙesu" Sai da aka ambaci Laila ne Gwadabe ya ɗago idanuwanshi da suka rine ya kalli Yaya Hambali kallon tsab. Ya dawo da kallonshi ga Babala itama. Ai ko karen haukane ya cijeshi ba ya auro Laila ya ajjiyeta a gidanshi matsayin mata ba. Yarinyar data kasa riƙe amanar aurenta take turo mishi da saƙonnin soyayya da igiyoyi uku a kanta itace zai auro ya ajjiye a gidanshi matsayin uwar ƴaƴa. A ɗauri kashi ko a ɓata igiya. Kab ƙauyan Takai waye bai san Laila ɓarauniya bace, ko ɓera sai dai ta zama yayarshi shi ƙaninta. Bai dai ce dasu uffan ba har suka gama maganganunsu da baya fahimtar komai suka fice. Toye ne ya fito daga ɗaki yace da Abbanshi. "Abba yinwa muke ji" Hannun yaron ya jawo ya ɗaurashi a cinyarshi yana kallonshi. Bakinshi irin na iyabo babu maraba, hawayen dake shirin zubo mishi yayi saurin ɗaukewa da hannunshi. "Bari in kawo muku abinci ko, ina Taiwo da Kahinde suke?" Ya tambayi yaron. "Suna ɗaki sai kuka suke yi" Ba shiri ya miƙe tsaye, hannun Toye ya ja suka shiga ciki. Taiwo ce take ta kuka ta kifa cikinta akan gado. Kahinde sai bubbuga bayanta yake yi yana gwarancenshi. MRS BUKHARI 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundation gidauniyar da muka buɗe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya. Waɗanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE) 300 kacal zasu iya kuɗin karatu NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 13 Tausayi gami da ƙaunar yaran ta shigeshi ainun. Harma yake ganin ganinsu ne kaɗai ka iya rage mai zafi da turirin rashin Iyabo. Haƙiƙa yayi rashin macen kirki, macen da tafi kowa sonshi da sanin hamimmancinshi. Ji irin wuya da ɗawainiyar da ta dinga yi a sanadiyyar ciwonshi. Amman ji irin sakamakon da su Babala suka yankar mata na tarwatsa duniyarta, tare da farraƙata akan ƴaƴanta da mijinta. Rungume yaran yayi jikinshi babu laka sam, rarrashin Taiwo yayi har sai da tayi shiru. "Toye zo ka kula dasu bari in siyo muku waina kuci" Yana faɗin haka ya fice, babu ko nera biyar a jikinshi, bashin mai wainar ta bashi na wainar hamsin, ya dire musu suka ci, suka sha ruwa. Fita yayi ya shiga kitchen ɗin Iyabo ya kunna risho ya ɗaura musu ruwan wanka. A kitchen ɗin yayi zamanshi tare da tariyo irin rayuwar da su ka yi da Iyabo, da irin nutsuwa da farin cikin da take samar mishi babu dare babu rana. Yana kitchen ɗin Babala ta leƙo da kwanon abinci a hannunta, ganin yanda yayi tagumi ya tusa risho a gaba ne yasa tayi turus a tsaye da kwano a hannunta. Yaran kuma tana jiyo ƙiriniyarsu. "Gwadabe au so kake yi tunani ya halakamun kai. Alhalin ita tana can hankalinta a kwance?. Yanzu me kake yi a ɗakin girki" "Ruwan wanka nake tafasawa zanyi ma yaran wanka Babala" Harara ta watsa mishi tare da cewa. "Ba cewa nayi maka zan tafi dasu ƙauye ba, ka ganni abinci na leƙo in ajjiye maka fa, sai in ɗebesu danyanzu zan juya yau muna da biki a gidan mai gari" Ajjiyar zuchiya ya sauke, tare da tasowa jiki ba kuzari, kirjinshi kuwa sai harbawa yake yi, zuchiyarshi na watsa jini jikinshi bisa rashin ƙa'ida. Hakanne ya haifar mishi da jin jiri da mashasshara mai zafin gaske, dan har hucin zafi yake ji a fuskarshi. Bakinshi kuwa tamkar maɗaci aka zuba mai haka yake ji. Inda Babala take tsaya ya isa. "Babala yarannan ni zan riƙesu da hannuna. Inaso zasu yi karatu mai zurfi ba zasu yi rayuwa a Takai ba. Kab yaran gidannan a cikin gidannan su ke rayuwarsu, wasu muna tare dasu, wasu kuma sun yi aure. Dan haka nima zan riƙe yarana" Babala tace. "Da kyau Gwadabe. Dama ni dan in tausaya maka in ɗauke maka nauyine a matsayinka na namiji. Amman tunda har kana ganin reno abune mai sauƙi, gaka ga yaran. In sun ga dama suga ƙarshen biro. Duk karatunsu ai basu isa ganin ƙarshen biro ba. Kuma ka shirya sati me zuwa ka tawo zance wajan Laila ka shiga sahun manemanta, dan manema sun yi mata ca a halim yanzu kowa so yake ya ɗauketa, ni kaga tafiyata" Ta dure mishi kwanon abincin nashi ta fice tana surutai tare da kutuntumawa Iyabo da yarenta zagi. Idanu Gwadabe ya lumshe kawai. Shi yaima yaranshi wanka fes, ya ja hannunsu har zuwa islamiyya kasancewar ranar asabar ce babu boko. A hanyar shi ta dawowane yaci karo da yaya Hambali a mota zai tafi kasuwa sai ya ɗan dakata. "Gwadabe daga ina kake haka? Kaga takalmin ƙafarka ɗaya naka ɗaya na matarka ne fa. An ya Gwadabe asirin da dangin Iyabo su kai maka ya gama sakar ka kuwa, sai kace wanda akace ma Babala ta riga mu gidan Gaskiya" Numfashi dogo Gwadabe yaja, ya kai duba kan ƙafafuwanshi, zahiri takalmin Iyabo ya ƙaƙaba a ƙafarshi duk rabin dunduniyarshi a ƙasa yake, takalmin ma kuma mai ɗan tudu. Ɗayar ƙafar kuma takalminshi taka teba ya saka. Allah yana gani baya cikin hayyacinshi balle har ya fahimci ƙafarshi a matse take, ko yaji yafi tuɗu ta ɓarayi guda. Murmushi kawai yayi. "Kaga yara na miƙa makaranta, bansan wari da wari na saka ba, hankali shine gani, idanu ƙululun kawai ne." Kallonshi Yaya Hambali yayi wata ƴar dariya harda shewa kafin yace. "To sai zuwa yaushe zaka soma zagayawa kasuwar, tunda dai sauƙi ya samu, kuma Iyabo data raɓeka ta raba mu da kai ta zama tarihi a rayuwarka. Kaga ai sai ka zo mu ringa tafiya kasuwa, kwanannan kaima zaka sai motar da kake so ka dinga tuƙawa" Murmushin yaƙe wanda yafi kuka ciwo Gwadabe yayi, yace. "Nagode da tayinka Yaya Hambali. Amman bana jin zan amshi wannan tayin naka. In na warware da kyau zan nemi sana'a dede dani in soma. In Allah ya dafa mini sai kaga na yi gida harda mota, yarana sun samu ilimi ingantaccen" Iyakar abinda Gwadabe ya furta kenan Yaya Hambali ya fusata har yana doka sitiyarin motarshi. "Ni kake faɗa ma magana haka gatse_gatse gwadabe? Ka mance sanda nake goyonka muje gona, nake cire kudina in biya maka kuɗin makaranta, in kama hannunka in kai ka makaranta. Kaci kasha naima sutura duk da dukiyata, kuma nake matsayin uwa da uba duka a wajenka? Ko Harisu bai isa faɗa mun maganar banza ba, balle kai wanda a haife na haifeka?" Sai zazzare idanu yake yi yana kumfar baki, Gwadabe dai baice mishi komai ba. Har ya gama hargaginshi. "Hmmm Yaya Hambali kenan. Shagone dai ni Gwadabe bana so bana buƙata. Bana nema a wajenka a wajen Allahn daya baka nake nema, kaima ba dabararka bace ta baka ba ka san da wannan." "To Shikenan na cire hannuna a kan ka tunda dai taimakonka da nake son yi ne baka so. Kaje kayi Abinda kake ganin ya dace da kai ba shikenan ba? Amman in sha Allah dakai da yin kuɗi har abada Gwadabe muddin ina raye baka ba yin arziki da Hambali kake magana, ɗan iska marar kunya fitsararre Allah dai ya kwashe maka albarka" Yana gama faɗan haka fuu ya ja motarshi ya buɗe Gwadabe da ƙura, ya cika mishi idanu fal da kasa. Idanunshi a runtse suke hawayen bakin cikin danginshi na tsiyaya a idanunshi. Shin wai me yasa ƴan uwanshi su ka fi sha'awar ganinshi a cikin halin damuwa da ƙunci ne, anya kuwa Babala itace mahaifiyarshi ta asali kuwa, ko dai shi ɗin ɗan riƙone bai sani ba? Amman da ace ɗan riƙone da dole ƙauye su sani domin a ƙauye kunne ya girmi kaka. A wajen Gwadabe ya ci alwashin bazai taɓa tambayar kowa komai ba, bazai karɓi ko ficika daga hannun kowa ba. Zai fita nema, kamar yadda Yaya Hambali ya fito nema shi shi kaɗai a shekarun baya, kuma Allah ya buɗa mishi. Shima Allah shine gatanshi ba Yaya Hambali ba, zai nuna musu shi namijine mai zuchiya ba mai hangen na wani ba. Idanunshi ya buɗe ya karkaɗe fuskarshi da idanunshi ya ci gaba da tafiya. Haka Gwadabe ya kwana a tsakiyar yaranshi, yanda rana ta kasance mishi haka darenma ya zame mishi. Sai juyi yake yi, yana tunanin irin rayuwar soyayya da kulawar da suka yi da Iyabo. Da irin abubuwan da akaita yi mata, kuma ta shanyesu duk dan ta zauna tare dashi. Amman daga karshen ƙarshe duk kiyayewarta sai da sakin ya afku a kanta. "Iyabo ina roƙa miki Allah ya baki mijin da zai jarabtu da sonki fiye dani, Wanda ya fini komai a rayuwa. Ya Allah ka kai baiwarka Iyabo gidan hutu da jin daɗi, mala'ikun Allah ku shaida ni dai a zamana da Iyabo babu cutarwa, kuma kune shaidar ni dai na ɗaga mata ƙafa dan ta shige aljanna. Allah ka haɗata da abokin rayuwar da zai ɗaga mata tashi ƙafar shima." Sambatu kawai Gwadabe yake ta faman yi kamar zararre. Haka Gwadabe yai ta tunane_ tunane har gari ya waye musu. Kamar jiya bashin wainar ya kuma karɓoma yara su ka ci ya kaisu makaranta Yana shiga gidan ya tadda dangin Iyabo suna tozarci a tsakar gidan. Sun zo dibar ragowar kayanta da yayi ragowa, da suturunta dai da kayan aiki haka. A wannan rana ya yasha zagi da ele a wajen su Iya Beji. Har tukunya Iyaa Kokodeen ta kwaɗa mishi a gadon bayanshi. Da yaga tozarcin ya isheshi sai ya koma ƙofar gida yai zamanshi. Yaya Hambali kuma sai sababi yake yi cewar duk Gwadabe ne sila, daya haɗe musu jini da jikokin oduduwa. Gwadabe na zaune a ƙofar gida ya hango Bara'u tafe. Ƙuri yayi yana kallon tahowar abokin nashi har ya iso gareshi ya zauna daf dashi. Amman fa kafin yace wani abu sai ga su Iyaa Beji sun fito suna zage_ zage Yaya Hambali na biye dasu shima sababin yake yi. Kan kace me unguwa ta ɗinke, mata har ta katanga leƙe suke yi, kunsan mata akwai gulma ko ince son ganin ƙwaƙwaf. basu dena baloƙoƙinsu na gado ba, sai da Yaya Hambali ya cukume Iyaa Beji, a tunaninshi zai daketa. Ai kuwa taron dangi suka haɗu suka yi mishi da ƙyar mazan unguwa suka karɓeshi a hannunsu duk haushin Gwadabe suka saukeshi akan Yaya Hambali. Bara'u da Gwadabe suna zaune suna kallon ikon Allah kawai. Yaya Hambali ya matso kusa dasu Gwadabe a zafafe yace. "Allah wadaran naka ya lalace. Kaji dai kunya Gwadabe ace waɗannan gayyar na aiya gayyar na yadadan sune surukanka. Mu kanmu ka cutar damu daka dage sai da muka haɗa iri da yarbawa. Duk irin matan dake cikin hausa Fulani ka rasa wacce zaka so sai Iyabo. Jibi yadda mata suka dakeni har suka fashe mun baki dan iskanci kuna zaune" Bushasshen yawu Gwadabe ya haɗiye muƙut. Bara'u ne yace. "Yaya Hambali ayi haƙuri. Komai ai ya riga ya daya ƙare. Allah dai ya ƙara rufa mana asiri" "Gafara can. Bara'u ai ko kisa Gwadabe yayi ba zaka iya ganin laifinshi ba. Aikin ɓur in ji tusa" Ya buga kafarshi ta dama a ƙasa, kana ya shige cikin gida. Bara'u ya sauke ajjiyar zuchiya yace. "Kayi haƙuri Gwadabe na roƙe ka da girman Allah. Ka ɗauka wannan ƙaddarace daga cikin sinnar rayuwa. Iyabo kai mata adda'a gaba Allah ya bata miji na haƙiƙa. Ni kuma da nazo da zummar in tafi da yaran duka can wajena Sakina ta haɗe da nata ta riƙe. To ina cikin mota sai Tamu yai kiran wayata Allah da ikonshi na kwashe zance tas na sanar mishi, to sai yace shi zai riƙe ƴan biyun a hannunshi zai sa su a makaranta. In kanaso zaka iya barinsu a hannunshi. In kuma kayi aure zaka iya zuwa ka ɗebi yaranka ka baiwa matarka taci gaba da kular maka dasu. To nasan zaka fi son yarannan a hannunka Gwadabe. Amman sauƙi muke nemar maka kayi haƙuri ni zan tafi da Toye tamu zai riƙe Taiwo da Kahinde, tausayin yaran muke yi a hannun su Babala. Na ji daɗin samuwar lafiyarka, babu abinda zamu ce da Allah zai godiya. Ka yi haƙuri ka daɗa" Wata wawuyar ajjiyar zuchiya ya sauke mai nauyi yace. "Bara'u yau ko ni kuka ce zaku ɗauka da kai da Tamu ba yaran ba, bana jin zanyi muku musu. Yarannan naku ne ku yi yadda kuke so dasu. Nagode da soyayya Allah ya bar zumunci. Sannan Bara'u wallahi na rungumi ƙaddarata, ina fatan Iyabo ma ta rungumi tata ƙaddarar. Amman fa ni da Iyabo Allah shi ya haɗa zukatanmu. Ko anan gaba in nayi aure, matar zata tsaya ne kan iyakar matsayinta, bata isa hawa matsayin Iyabo ba. Ita kanta nasan hakanne ta ɓangarenta. Bara'u Iyabo mutum ce har da ɓari" "Zahiri Iyabo Mutum ce guda da ɓari. Allah yai mata sauyin alkhairi, kaima Allah yai maka sauyin alkhairi. Yanzu mu je mu shirya yaran, tunda jikinka yayi kyau ai sai mu je Abujar tare mu kai ƴan biyun. Daga nan sai mu wuce Takai. Dan Malam magaji ya zo jiya. Inajin su Yaya Hambali basu sani ba tukunna dai" Ai kuwa haka akayi. Bara'u da kanshi ya haɗa ma ƴan biyu kayansu a jakar buhu, ya haɗa na Toye. Gwadabe ya rufe ɗakin da ko tabarma babu. Yaima su Yaya Hambali sallama kan zashi Abuja daga can zai zarce Takai gaishe da Baba Magaji da yazo. Yaya Hambali yaso jin dalilin tafiyar, amman Gwadabe sai ya ɓoye mishi dan ko fuska bai bashi ba, yana kan turmi Yaya Haula na gasa mishi baki. Bara'u shi ya biya misu kuɗin mota. Cikin Awa shidda sai gasu a Gwagwalada. Da mota Tamu yazo ya ɗaukesu har zuwa dan madaidaicin gidanshi. Bayan sun yi sallah sun huta, Ayashe ta kawo musu abinci Falo ƙanwar Tamu na biye da'ita da plate a hannu. Ayashe ta shiga da yaran ciki, bayan ta jajantama Gwadabe abinda ya afku cike da jimami. "Kaga Shafs ce wannan data shiga ciki yanzu. Da shine nake tunanin Bara'u ba zan ba Gwadabe Shafa ba kawai. Kaga a matsayin wa kake a wajenta, kuma ta ɗanyi karatunta yanzu haka karatun diploma take haɗewa anan Gwagwalada. Da in ta kammala sai ayi auren ko ya ka gani Bara'u?" Bara'u yayi dariya suka tafa da Tamu kafin yace" "Yarinya zuƙeƙiya son kowa, gata budurwa sharab. Shafa a gabanmu aka haifeta. Bana mance taron sunanta, kasan gida _gida mu ka dinga bin abokanmu muna raba musu alawar gaiyata. Kowa yazo da sile da sisinshi. In abun ya tabbata zaiyi kyau sosai " Tamu yace. "Wato kai Bara'u baka da mantuwa sam. Ni ai tunanina in rama halaccin da Gwadabe yayi mini, ko banyi mai daidai da abinda yayi mun ba, in kamanta mishi. Gwadabe na baka Shafa halak malak. Nine maɗaurin aurenta dama. Zan mata bayani duk lokacin da ka samu nutsuwa sai ka neme ta, a hankali tunda ba sauri akeyi ba sai ku daidaita tsakaninku. Yara kuma zanci gaba da riƙonsu ko kun yi auren ma, in sha Allah ni zan aurar dasu da hannuna. Zan kuma so in haɗe su aure da nawa yaran dakan ɗaka shiƙan ɗaka" Gwadabe bai yi musu jayayya ba bare turjiya. Kwana ɗaya su kayi a garin Gwagwalada suka juya washe gari, bayan Gwadabe yayi sallama da ƴan yaranshi, abinka da yara sun shige cikin yara ƴan uwansu sai adabo ma suke ma uban. Ganin yaran sun sake ne uban ya ɗan ji ƙarfin guiwa kuma. Ruga Iyabo:. Tabarma Daso ta ɗauko ta shimfiɗama Yaya Hamma daga can gefe guda. Jatau ne ya shigo da garken shanunshi guda yana tafe yana waƙar fullanci, hannunshi da ƴar tsaraba. "Jatau yau kai ka soma shigowa gidan?" Da Hausa tayi mishi wannan tambayar. Shi kuma hankalinshi duka yana kaina, ina son in ɗebo ruwa a randar ƙasa in kawo ma Yaya Hamma. "Baƙuwa mu ka yi ne Daso?" "E baƙuwa ce kuma ƴar gida, Yayar su Boɗɗo ce tazo daga birni" Sai ya washe bakinshi muka gaisa cikin girma da arziki. Na dure ma Yaya Hamma ruwan sha a gabanshi na koma kan turmi na zauna. Jatau da Hamma nan suka kacame da yare, daga bisani Jatau ya wuce da shanunshi izuwa maɗaura. "Jabu zo ki zauna sabida ke nazo gidannan da yammannan" Daso dake hura wuta tace. "Ko ni na faɗa a rayina, sabida Jabu ne kazo Yaya Hamma" Sai tayi murmushi, nima murmushin na mayar mata, na ƙarasa kan tabarmar da Hamma yake na zauna a gefe. "Na ji labarin mutuwar aurenki ƙanwata. Abun ya dake ni ainun, naji tausayinki sosai. Amman mu zamu baki farin cikin da har sai kin mance da komai a matsayinmu na dangin uwa, muma zamu taka tamu kalar rawar, tunda kika zaɓi ki rayu damu a ruga, kika haƙura da rayuwar maraya duk da acan ki kai wayau. Kiyi haƙuri kinji am?" Wasu hawaye ne suka gangaro mun. Ban aune ba sai kuka mai gunji ya tawomun babu zato. A tiɓi tiɓi_tiɓi da kayan mazaunai na shige bukkarmu na zauna akan gadon ƙasarnan na shiga sana'ar kuka. Wani tuƙuƙin baƙin ciki da takaici sai yanzu ne komai ya soma dawo mini. Kuka na zage nayi na ban mamaki. Ƴan uwana suka bani sarari na dirji kukana yadda yayi mun nayi shiru dan raɗin kaina. Sai zuchiyata ta ɗan washe ta rage nauyi. Na yi zaman tunani a zaune bansan iyakar adadin ba. Sai shigowar Yafendo na gani kawai. Da sauri na share guntun hawayena ina duban fuskarta. Sai naga fuskarta cike da damuwa, da dukkan alamu damuwa da damuwata ce take yi. Ledar hannunta ta miƙo mun nasa hannu na karɓa kafin tace. "Ban isa hana ki kuka, ko hanaki damuwa da tunanin yaranki ba Jabu. Kinga Daso tun bayan rasuwar mijinta kullum sai ta yi kuka zuchiyarta babu daɗi. In Hamma yazo gidannanne ma take samu tayi farin ciki. Ni kuwa ban taɓa hanata kuka ba. Rabuwa da miji ciwonshi bashi da misali sam, musamman mijin da kuke soyayya da zaman lafiya. Ace mutuwace tayi muku yankan ƙauna. Ko kuma wata ƙaddararce ta raba ku ba da son rayukanku ba. A lokacin da mahaifinki ya rasu Adda Daso ta shiga wani irin mawuyacin hali. Mahaifiyarki har jinya sai da ta kwanta na tsawon wata shida masu kyau. Har gaban abada ba zata dena tunanin mahaifinki ba. Musamman data haɗu da azzalumin namiji magoki. Da girmansu haka bai bar dukansu ba. Zuwan da ki kayi ma dan kawai ta roƙeshi ya barki ki zauna a wajenta har ki gama kwanakinki ki tafi. A daren zagi da cin zarafi babu wanda baiyi mata ba, har marinta sai da yayi" Da mugun sauri na ɗago. Wata kibiya ta soki ƙawon zuchiyata, siraran hawaye suka gangaro kan kumatuna masu zafi. Yafendo yanzu kamar Dada da girmanta da yaranta manya sai mijinta ya daketa harda zagi, a halin da take rayuwa kenan?" Zama Yafendo tayi a kusa dani tace. "A haka Adda Daso take rayuwa da azzalumin mijinta. Har da tsohon ciki a jikinta dukanta yake yi. Ko a cikin Boɗɗo yayi mata wani dukan da tai ta zubar da jini, duk muka cire rai da cikin. Sai daga baya cikin ya tashi. Amman sai da Boɗɗo ta shekara biyu cir a kwance a cikinta kafin ta haifeta. Wannan kuma ana tunanin da sa hannun uwar gidansu akan lamarin. Kuma ya karɓe shanunta na gado ya haɗe da nashi shanun, Adda Daso bata ribatar komai. Shanune masu tarin yawan gaske, kinga gaa nawa garken can Jatau ya dawo dasu, sai hauhawa suke yi. Ita kuma bata san adadin yawan haihuwar da nata shanun suka yi ba, dan nata mata ne, namijin guda ɗaya ta samu. Ke Jabu in nace zan ta baki tarihin mijin mahaifiyarki zamu kwana mu wuni a nan bamu ƙare ba. Shi yasa ko da yaushe take cike da tunanin marigayi mahaifinki. Soyayya da kulawar daya bata ne, yasa ta fifita soyayyarki fiye da soyayyar duk yaranta. Duk ɗan abinda ta samu burinta ta tara in zata kai miki ziyara ta miki hidima, kinji na rantse miki tun bayan rasuwar mahaifinki ban sake ganin annuri akan fuskar Adda Daso ba, sai yau data zo gidannan tana sanar dani zuwanki garinnan, damma a hakan ta kwana cikin tashin hankali akan mijinga." Kukane yaci ƙarfina, zuchiyata sai luguden daka take ta faman yi. Ina jin duniyata na wujijjiga rayuwata. Tausayi da zunzurutun kaunar Dada ya sake ɗamfaruwa a raina. Yafendo ta dafa ni nayi firgigit na kalleta. "Ki tashi ki ɗauro alwala ki yi sallah. Wannan ledar dana baki Hamma ne ya ce a baki. In ki ka yi sallah sai ki fito tsakar gida in gabatar dake ga ƴan uwanki" Jikina a sanyaye na ɗauro alwala nayi sallah. Na daɗe ina adda'a, a lokacin zazzaɓin dake jikina ya rabkeni ainun, ko idanuna bana iya buɗewa. A halin da Daso ta shigo ta same ni kenan. Abu kamar da wasa_wasa sai na rasa numfashina, jikina kuwa kamar garwashin wuta. Sai da na shafe tsawon wata biyu da kwana goma sha ɗaya cur a kwance babu lafiya, sai maganin gargajiya akeyi mun, hatta ruwan wankana da ganyen magani a ciki, kuma Yaya Hamma suke kawo mun magani da ɗan abinda zan sa a bakina, Yaya Jatau ma yana kawo mun ɗan abun kwaɗayi, matarshi ma kullum zata shigo ta duba lafiyata, kuma in Yafendona, da Daso sun tafi tallen Nono, Hari itace ke zama dani matar Jatau. A wannan jinyar naga gatan dangin uwa. A wannan kwanciyar sai da dangin Dada suka zo kab suka gaisheni da jiki, a lokacin na gansu suka ganni. Dada kuwa kullum cikin suntiri suke ita da su cubu da Yusufu, Boɗɗo kuwa da hama suma kullum babu fashi sai sun zo dubani. " A cikin wata uku cib jikina yayi ƙwari babu laifi, lokacin iddata ta cika cib, lamarin da ya ɗan ƙara jagula lafiyar jikina kenan, sai da Yaya Hamma ya dinga bani baki, tare da lafuzza tausasa, har mamaki nake yi in naji yana furta wasu lafuza masu kwantar da zukata. Da yamman wata asabar bayan Daso ta dawo daga tallar nono muna ɗaki mu na ɗan taɓa hira, fuskarta cike da farin cikin ganin jikina yayi kyau yau. Duk da na rame fiye da tunanin masu karatu, fuskata ta yi fayau. A jinyar dana kwanta na samu kulawar mutane uku da bazan mance da hidimar da su kai mun ba. Daso, Yaya Jatau, Yaya Hamma. Duk kwanan duniya Daso itace mai bani abinci a baki, tare da gyara mun kwanciyata, ko amai nayi itace ke kwashewa. To a wannan kwanciyar jinyar nayi jinin al'ada hatta da tsumman jini da ɗan kamfaina Daso ke wanke mun da ruwan toka ta shanya su, wanda zai maka irin wannan aikin ba ƙaramin masoyinka bane. Yaya Jatau kuma kullum in zai dawo daga kiwo yana kawo mun wani gashasshen hanta mai yaji, shi nake ci da daddare, shi kaɗai ne nake iya ci ba tare da naji tashin zuchiya ba. Yaya Hamma kuwa shi ya dinga bin ƙauyuka ruga_ruga dan sama mun magani, wani gari wani ganye, ko kiwo yaƙi ya mai da hankali akai har sai da ya ga samuwar lafiyata. Kuma kullum a cikin yi mun nasiha da tattausan laffuzza yake. Muna ɗan hirarmu muka ga an buɗe labulen kaban dake ƙofar bukkarmu. Yaya Hamma ne ya shigo hannunshi riƙe da kwano. Daso ce ta miƙe ta karɓi kwanon ta dure a gabana tana dariya tace. "Nasan ai nata ne ko Yaya Hamma? Shi yasa na dure mata a gabanta" Dariya yayi tare da nunata da yatsa yace. "Kin ganki akwai zolaya. Ai itace marar lafiya a gidan, shi yasa na kawo mata tasha romo" Sai tace. "Nima in na kwanta jinya ashe zaka kula dani sosai irin kulawar da ka ba Jabu?" Dani da'ita duka sai muka kafe shi da idanu. Sai da ya zauna a ƙasa ya tanƙwashe ƙafarshi kana yace. "Ai kamar ratayayyen hakkine a kaina in kula daku, ko da a gidan mazajenku kuke balle kuma kuna gabanmu. Jabu ya ƙarfin jikin, yaya haƙuri ds rayuwa, da haƙurin zaman ƙauyanmu mara wuta balle ruwan daɗi?" Ɗan murmushi nayi nace. Jiki Alhamdulillah sauƙin yana samuwa sosai. Babu abunda zance sai godiya. Kuma ina godiya da wannan ɗawainiya da kukaita yi dani" Bayan na bashi amsar na sauke kaina ƙasa. "Ai ya zame mana dole, ki daina godiya ma Jabu" Miƙewa tsaye yayi. "Ba dai tafiya ba?" Cewar Daso. "Tafiya zanyi. Dama abinci na kawo mata. In kuma ƙara ganin jikin nata. Amman dai ku shirya zuwa dare zan zo mu leƙa dandali Jabu taga yadda muke wasanninmu gwanin sha'awa, wala Allah hakan ya rage mata raɗaɗi." Dariya nayi musu kawai. Aini na rabu da nishaɗi tunda na rabu da Gwadabe, dan nishaɗi na wajen tsuntsun soyayya. Amman a fili saina amsa da cewa. Allah ya kaimu" Ko dan in ƙarfafasu tunda burinsu suga na saki jikina na mance komai. Da haka mu kai Sallama, bamu muka fito daga cikin bukkarmu ba saida mu ka sallaci sallar isha. A tsakar gida muka ci fsrfesun da Yaya Hamma ya kawo mini harda Yafendo da Jatau, dama Hari Matarshi. MRS BUKHARI ce. *Ƴar uwa ina fatan baki mance da kayan ƙamshin Mrs Bukhari gidan ƙamshi ba ko? Ƴar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ƙamshi. Matso kusa ƴar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ƙamshi ya riƙe miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake saƙawa a tsakankanin kaya. Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ƙamshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata. Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haɗe da turaren fesawa a gashi. Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ƙara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ƙamshin kifi ɗanye. Inada humrori kala_kala. Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ƙamshi. Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ƙamshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ƴar mutan Maiduguri kin samu ƙamshi. ( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai ɗauke da abubuwa huɗu manya kuma a kan kuɗi ƙalilan karki bari garaɓasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)* NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM 14 Muna gama ci sai ga Yaya Hamma ya shigo. Yana saye da wani yadi mai ruwan bula ɗinkin ƴar shara, yadinnan duk ya gaji yayi laushi sosai sai laɓewa a jikinshi yake yi. Wandon jikinshi kuma na koren yadi ya saka ya ɗauko hular tashi ka fiye naci irin hular da fulani suke mugun so ɗinnan ƴar madina mai fara da baƙa a jiki, ƙafarshi kuma saye da takalmin roba mai ruwan bula duk ya fashe, sai ƙamshin wani turare mai gafin ƙamshi yake yi, daya isa wajensu Yafendo dake akwai fitilar aci bal_bal na gango kwalli rambaɗe a fararen dara_daran idanunshi har zazzagowa yayi. Bayan ya gaisa dasu Yafendo yayi ma Baba bayanin yazo ya kaimu dandaline, sai ya fita waje ya bamu sarari dan mu kintsa. "Daso maza ku tashi ku shirya abun nema ai yau ya samu ko?" Dariya mu ka yi mata kawai. Ni dai mayafi kawai na ɗauka, saye nake da koɗaɗɗen riga da zane. Saɓanin Daso da sai da ta shafa kwalli harda janbakin majigi tasa ma labɓanta. Cikin zaulaya nace. Harda kwalliya ko za'a samo mana bazawari ko?" Dariya tayi kawai tace. "Kayya, ai tunda na rasa Chubaɗo ban sake tsaiwa da kowa ba. Ni abunma wani iri ba fasali yake yi mini" E dole zaki ji banbarakwai wai namiji da suna Hajara. Amman ya muka iya haka Allah ya zaɓar mana. Fatan shine Allah ya sadamu da mazajen da zasu ji tausayin rauninmu. Gara ma ke Daso mijinki rasuwa yayi fa. Ni fa Gwadabe yana doron duniyarnan rabamu akayi a bisa tursasawar mahaifiya da danginshi" Siraran hawayene ban aune ba suka biyo kan kuncina. Dafa kafaɗata Daso tayi jikinta a mace tace. "Mu yi haƙuri kawai mu rungumi ƙaddararmu. Allah yana sane damu, bai mance mu ba. Ta yiwu ya shirya mana kyakkyawar rayuwa a gaba. Ta yiwu kuma wahalar rayuwarmu ne zai fara. Amman duk abinda ya samu bawa ya fauwala shi ga Allah " Wannan gaskiya ne. Muna fatan kyakkyawar rayuwar a gaba. Allah ya sadamu da mazajen da dan so zasu ji kamar su mallaka mana numfashinsu dan mu daɗe mu yi ƙarko. Mu je mun bar Yaya Hamma a waje yana ta faman jira" Kafinma in rufe baki muka jiyo Yafendo tana kwaɗa kiran sunanmu tana yaren Fullanci. Ba shiri muka fito tare da ficewa a gidan. Ko da muka kama hanya, sai cin karo muke yi da mata da samari suna nufar dandali. Ina gefen hannun daman Yaya Hamma, Daso na gefen hagunshi mun sanya shi a tsakiya. Sai hira yake janmu dashi, Daso ce ke bashi amsar duk abinda ya tambaya. Ni tunanin Gwadabe da yarana, da kuma tunanin ta wacce hanya zanbi dan ganin na sanya Dada a farin ciki dariya da walwalarta ta dawo kawai nake. Wani shashe na zuchiyata sai kawai katsaham yace. "Me zai hana ki nemi Uwani in dai bata tafi ba, kema tayi miki hanya ki tafi. In kika tara kuɗi ne kawai zaki iya ɗauke mahaifiyarki ki rabata da azzalumin mijinta, ki kuma rabata da tallan Nono. Wannan shine hanya mafi sauƙi. Tunda ba kya kashe mata aure ba tare da kin shirya mata gidan da zata rayu da yaranta ba, kuma ba zaki hanata tallan nono ba har sai ke kin samu abun yi, ko kuɗi a hannunki da zaki ma rayuwarta hidima kamar yadda mahaifinki yayi mata kafin ya rasu" Nan take sai nake ganin kamar ma na samu mafitar cire Dada cikin ƙangin rashin ƴancin da take ciki. Dan a shirye nake ko matakin shari'a ne zan bi muddin yaƙi sauwaƙe mata igiyar ƙaddararran autenshi. Lokacin dana kwanta jinya take yawan sintirin zuwa dubani. Cubu ranar ta shigo da kuka take labarta ma Yafendo cewar Dada tana gida Baffansu ya daketa ya kumbura mata fuska, sabida sintirin zuwa dubani da take yi wai ya isheshi sai kace nice kaɗai ƴar data haifa. Lamarin da yasa ƙannena suka haɗe kansu suna kuka, tare da adda'ar Allah ya kawo ma Dada mafita ya cireta a wannan ƙangin. Daga ranar kullum ƙwaƙwalwata cikin tunanin sama ma Dada mafita nake, ko da kuwa zan rasa tawa mafitar. Sai yau Allah yayi na tuna abinda nake ganin zai iya kawo ƙarshen hawayen Dada. Tafiya Kano ya kamani gobe da izinin Allah, dan bahaushe gwanin iya tsara zance cikin hikima da azanci yakance da zafi zafi ake dukan ƙarfe, ko kuma yace da safe ake kamun fara" "Jabu tunanin me kikeyi haka mai zurfi har mun iso dandali baki sani ba? Na lura jefa ƙafafuwanki kawai kike yi" Cewar Daso wacce ta kafeni da idanu, Yaya Hamma shima ido ya zubamun, suna sauraren abinda bakina zai furta da sunan amsa. Iska na jawo daga huhuna na furzar kana nace. Tunanin rayuwa kawai nake yi Daso. Ai baka isa ka raba zuchiya da tunani, ko da ayyane_ayyane ba" Na ja bakina na tsuke. Na kura maa wutar karar dake ci bal_bal a tsakiyan dandalin ido, wajen yayi haske sosai ina iya hango kwalliyar mata da maza. Wutar nake kallo yanda take tartsatsi. Amman abinda zuchiyata take ciki yafi ƙarfin tartsatsin wutarnan, jin zafi nake yi daya wuce doka da oda. Hannuna Daso ta kama muka nemi wani benci da babu kowa muka zazzauna. Ƴan berorin ƴan mata sai wasannin gaɗa da waƙe_waƙen su na fulani suke yi. Samari sun kewayesu sai tafi da ɗaga sandunansu suke yi. "Kinga dandalinmu ko Jabu?, Allah yasa wasannin al'adunmu sun burgeki?" Cewar Yaya Hamma wanda yake zaune kusa dani. Murmushi kawai nayi mishi na sauke kayina ƙasa ina kallon yatsun ƙafata. "Jabu tunanin menene ya bujuro miki duk ya sauya kamanninki? Kinga lafiya abun tattalawace ga duk wani rayayye. Me zai hana ki tausaya mana ki dena wannan tunanin ko dan lafiyarki da farin cikin masu son ganinki cikin ƙoshin lafiya?" Kallonshi nayi na mai murmushi idanuna cike da ruwan hawaye. Shima murmushin ya bini dashi, kafin ince wani abun sai ga wani matashi ya ƙaraso gabanmu da sandarshi rataye bisa kafaɗunshi. "Hamma in babu damuwa inaso ka bani dama mu zanta da Daso. Na jima ina bibiyarta domin ta bani damar ko sauraren abunda ke tafe dani taji amman ta ƙi ya" Yaya Hamma ya dubi wannan matashin, ya dubi Daso wacce ta turɓune fuskarta kamar bata dariya. "To jeka zata zo yanzu. Kuma ni Hamma na baka damar zuwa zance wajen Daso Manga daga yau kuma yanzu. Daso tashi kije Manga zai yi magana dake" Nasan ganin rashin wasa gami da murtukewar fuskane yasa ta bishi ba dan ranta ya so hakan ba. Tafiyarta ke da wuya Yaya Hamma ya ce. "Bani labarin abinda yake damun zuchiyarki. Nayi miki alƙawarin magance miki matsalar duk girmanta" A'a Yaya Hamma babu komai. Ni dai inaso gobe zan je garin Kano. Amman nayi maka alƙawarin kwana biyu rak zanyi zan dawo." Da sauri ya kalleni har tsoron da yake son ɓoyewa ya kasa ɓoyuwa. "Kano kuma, ba dai wajen tsohon mijinki kike son zuwa ba, ko ganin yaranki ba? Kinsan yin hakan a wannan halin da kike ciku ka iya fama miki ciwon dake zuchiyarki" Da sauri na katseshi da cewa. Ko ɗaya ba abinda zai kaini Kano ba kenan. Akwai wani shiri da nake son in yi ne a can Kanon. In abun ya tabbata kaine mutum na biyu da zan faɗa ma bayan Daso" Ajjiyar zuchiya ya sauke yace. "Au ashe Daso ta fini matsayi a wajenki? Sai ta sani kafin ma in sani ko. Nagode" Yanda ya turɓune ƴar kyakkyawar fuskarshi sai ya bani dariya ainun. Ba haka nake nufi ba. Sabida ita ɗakunmu ɗaya da'itane. Amman kana da matsayi a wajena gaya. Ko tafiyar nan da zanyi gobe babu wanda na sanarma sai kai. Sai mun koma gida zan sanarma da Yafendo" Daɗi yaji sosai, sai kuma naga damuwa ta maye gurbin daɗin. "Allah yasa ba ƙauyenmu bane ya isheki kike son komawa maraya ba, sai da muka shaƙu dake kike son ki gudu ki barmu da kewa." Daso ce ta dawo ta zauna jagwab a gefena tana rishin kuka. "Ni Yaya Hamma bana son Manga. Bazan iya rayuwar aure da abokin Chubaɗo ba, gani zanyi kamar naci amanar Chubaɗo ne. Gashi kai kace ka bashi izinin zuwa zance, kuma kab garinnan waye baisan zafin kishin matar Manga ba. Ni ban shirya jefa rayuwata a cikin haɗari ba gaskiya " Dubanta yayi ranshi a bace, ko me ya tuna oho sai ya shiga aikin rarrashinta gami da yi mata nasiha. Mijintane dai ta rasashi har abada, ya zame mata dole yin sabon aure ko ba dan sha'awa ba ko dan tsira da mutunci. Ya ɗaura da cewa. "Kuma kinsan Baba ba zuba ido zaiyi ya barki kita zama a gabanshi babu aure ba ko. Lokacin da zai matsa miki da fito da miji nake jiye miki, dan in baki fitarba al'ada zata haɗaki aure da wani ɗan uwanki ko kina son hakan, ko bakya so. Ni abinda nake jiye miki kenan. Sannan Manga kab Rugar nan ansan mutumin kirki ne, gashi da yawan shanu, kuma jarumine sosai. Ko wacce bafulatana burinta auren jarumin namiji." Zaman dandalin dai haka muka ƙareshi babu armashi, Yaya Hamma ya mayar damu gida. Muna shiga a daren na sanar ma Yafendo inaso zanje Kano in Allah ya kaimu gobe, kwana biyu zanyi. Sai da ta ɗanyi jim kamar ba zata yarda ba, kamar tana son tambayata Allah ya soni bata tambayeni ba, sai cewa tayi dani. "Allah ya kaimu goben cikin rayayyu, sai ki shirya da wuri tafiyace mai nisan gaske" Da tunanin tafiyar na kwana a raina harma da mafarkin wai naje amman ban samu Uwani ba sai Hafizu mijinta. Washe gari tun asussuba nayi wanka. Ina yin sallah na fito da ƴar jakata ta hannu da kuɗaɗena a ciki. Kaya ko kala ɗaya ban ɗauka ba, nayi musu sallama akan zan biya wajen Dada da Boɗdo mu yi sallama. Daso ce ta fito domin yi mun rakiya. Muna fitowa muka ci karo da Yaya Hamma a zaune a bakin wata bishiyar darbejiya yana kallon ƙofar gida yaga yaushe zamu fito. Ba Daso ba ni kaina nayi mamakin ganinshi a wajen. Dan sai da nayi turus. Tasowa yayi ya nufo inda muke. "Yaya Hamma kaine da sassafe haka a ƙofar gida, zaman me kake yi a wajen?" In ji Daso kenan. Dariya yayi mata kawai kafin yace. "Tunda dai Allah ya ƙaddari ganawarmu ai shikenan. Babu gaisuwa sai tuhuma ko? Da fatan kun tashi lafiya" Muka amsa a tare, sannan mu ka gaisheshi cikin girmamawa. Gidansu Yaya hamma muka soma zuwa. A ɗakin Yafendo muka zauna, a gurguje mu ka gaisa na sanar mata inaso zanje birni amman kwana biyu zanyi. "To Allah ya dawo dake lafiya. Hamma sai ka kaita har tasha ka tabbatar motarsu ta tashi kafin ka dawo. Allah ya tsare. Hama da Boɗɗo suna garken shanu kuje ku samesu ko? Ke kuma Daso kizo in kin taso tallan Nono zamu yi magana muhimmiya dake" Kan Daso a sinne ta amsa da "To Yafendo" A garken shanu muka yi sallama da Hama da Boɗɗo. Sai adda'a su ke yi miki, daga nan sai wajen Dada. Ni da Daso ne muka shiga, Yaya Hamma fur yaƙi shiga yace Baffa faɗane dashi bai fiye son baƙi suna shigar mishi gidanshi ba. Mu ma muna shiga ya taremu harda sanda kamar zai dokemu. "Kai ku tsaya nan kar ku sake ko taku ɗaya a wajen" Ya faɗa da fillanci, Daso ce ta fassaramun abinda yace. Wannan kalma daya faɗa kamar ance Dada ta fito ta duba sai firit ta fito daga bukkarta. Su Cubu kuma da su Yusufu suna tsakar gidan, suna aikin dafa madara. Da sassarfa ta iso inda yake tsaye. Wallahi ɗaga sandar shi yayi kamar almara sai ya kwaɗa mata a goshinta jini ya yayi tsartuwa har a hijabina" Cikin hargagi yake yi mata magana da fillanci. Hannunta ta dafe da goshinta ta yi saurin juyawa, na fahimci umarni ya bata. Yusufu da Cubu ne suka yi kanta Cubu ta riketa zuwa ƙofar bukkarta. "Ku je Jabu. Zan dinga zuwa dubaki. Na mancene ban sanar miki ba ya kafa dokar kar ƙafarki ta tako mishi gidanshi" Da yarbanci tayi mun Magana. Ajjiyar zuchiya na sauke ina hango irin yadda sandar ta sauka a goshinta, ba tare da wani babban daliliba, ko da dalili addini ya bada umarnin a daki mace har a zubar mata da jinine? Ko da ma suna da ƙarancin ilimin addini, rayuwarsu a kiwo da tallar Nono take ƙarewa. Ji nayi na sake jin ƙarfin guiwar hukuncin dana yanke dan cire Dada a cikin wannan uƙubar. Hawayen daya zubomun nake shirin gogewa Baffa ya ɗaga sandarshi ya sauke mun a kafaɗata, zafin ya ratsa dukkan ƙasusuwan jikina kau,. Kafin in tantance tsakanin mamaki da tsoro naji Daso tayi ihu ta jani mun rufa waje a guje. A guje muka wuce Yaya Hamma. Sai biyo mu yayi da sauri yana tambayar ba'asin abinda ya haddasa gudun. Daso ce ta bashi labarin abinda muka tarar. Ni kam hawaye kawai nake sharewa ina kallon mayafina da jinin Dadana a jiki, sanadiyyar zuwa ganinta kawai aka zubar mata da jini. "Jabu kiyi haƙuri. Mu kanmu mun rasa yanda zamu yi mu tsamo Dada daga cikin halin da take ciki a wannan gidan. Amman abinda nake so dake shine dan Allah ki taya ta da adda'a, kuma zan baki shawarar kada ki sake zuwar mishi gidanshi, Dada zata zo har inda kike ta dubaki. Kar hakan yasa in kika tafi ki ƙi dawowa, hakan ka iya jefata a halin da yafi wanda take ciki yanzu. Zamanki tare damu zai iya kawo mata sauƙi sosai, kece babba ke zaki dinga rarrashin ƙannenki, kinga Boɗɗo kullum a cikin kuka da damuwar da Dada take ciki take." Ajjiyar zuchiya na sauke kawai nace. Babu komai, nagode da shawara. Daso ku koma daga nan ni zan tafi" "A'a ai kinji abinda Dadanmu tace dan haka har sai na tabbatar da fitar motarku a tasha. Daso ki koma gida ke" A wajen mu kai sallama da daso. Ni dai har muka gama wannan gwajab_gwajab ɗin fita zuwa gari hankalina baya ma tare dani. Wai duk haka Aure yake cike da ƙalubale kowa da irin nashi? Oh ya Allah ka kawo mafita a zamantakewar aure, ya Allah ka ba ma mata mafita. Har muka shiga cikin babbar tashar Adamawa babu wanda yace da wani ƙala a tsakanin ni da Yaya Hamma, dukkanmu sai tubka da warwara kawai muke yi, tare da karanta wasiƙar jaki. "Fullo Kano ne, ko Kaduna, ko Zaria ga motar Haɗejiya?" Cewar ma'aikatan tashar da suka nufo kanmu har suna rige_ rige. "Kano zata je, nawa ne kuɗin motar?" Cewar Yaya Hamma, tare da cusa hannu a aljihunshi. "Nera dubu da ɗari biyu zata biya" Kuɗin ya zaro ya kirga ya basu, ni kuma ya miƙo mun dubu da ɗari biyar. Ƙin karɓa nayi, ya dubeni rai a ɓace yace. "In baki karɓaba zaki barni cikin damuwa, da kokontan dawowarki rugar mu. Ni kuma dana tuna zaki iya ƙin dawowa, ko zaman rugarmu ya isheki take sai inji fargaba ta dirarmun. Jiya ɓarawon baccine ya ɗebeni shima cike da mafarkai akan tafiyar taki. Ungu kuɗinnan ko tsaraba kya yi musu" Nagode sosai Yaya Hamma, in sha Allah bazaan wuce kwana biyun ba. Kuma dan Allah ka je ka dubo Dada, ko a ɓoye ne ka kai mata magani, kai mata bayani kwana biyu zanyi" Yaya Hamma bai bar tasharnan ba har sai da ya ga fitar motarmu. Sai da motarmu ta yi nisa sosai na dena hango hannun Yaya Hamma a sama yana yi mun Adabo., ban dena waige ba har sai da na dena hango shudiyar rigarshi, Ajjiyar zuchiya na sauke na lumshe idanuna ina tunano yanda Baffa ya kabɗama Dada sanda. Wannan dalilin ne yasa kullum in zanga Dada sai in ganta cikin rashin guzari da rashin walwala, kullum cike take da tunani. Ta haɗu da azzalumin miji mai kafiya, tallar Nono ya cinye mata lafiyarta da kuzarinta. A shekarunta ya kamata ace tana zaune a nutse yaranta na hidinta mata, ba wai tai ta fita tallar nono, kuma mijinta na cin zarafinta harma da fitar mata da jini. Wallahi da Baffa zai iya amincewa in fanshi tallar Nonon Dada, da tuni na famsheta na zama ƴar tallar Nono kamar yadda ya zama al'adar matan fulani musamman mazauna rugage. Ya zame mun dole in yi duk abinda ya dace dan ganin na kawar ma da Dada Ƙwallar data daɗe tana zuba a idanunta. Gaga_gaga haka mukaita cin hanya, azahar, la'asar sai dab magriba muka shiga garin Kano, a unguwa uku muka sauka, ina fitowa titi na samu Bus har ƙofar layinsu Uwani. Na ko yi sa'a tana gida, tana tsakar gida tana kwasar tuwo Hafizu kuma yana shanya kayan yara a igiya. Tana ganina ta sau marar hannunta ta miƙe a zabure. "Iyabo kece haka afujajan?" Tana faɗin haka na fashe mata da kuka a tsakar gidan kamar ƙaramar yarinya. "Uwani jata kuje ciki maza" Cewar Hafizu. Hannuna Uwani ta ja muka shiga ciki, wallahi na fi minti talatin ina kuka take zazzaɓi mai azabar zafi ya rufeni. Uwani da Hafizu suka rufu a kaina suna ta rarrashina da ƙyar na haɗiye kukan nawa bakina na ambaton Allah. Ganin na ɗan samu nutsuwane Hafizu ya fita ya bamu waje. "Kawata lafiya kuwa kinga yanda ki kai baƙi kika rame kuwa? Gabaki ɗaya kin koma wata ƴar ƙauye, meke faruwa haka?" Cikin shessheƙa nace. Labarin da tsayi Uwani, amman bari in rama sallolina sai mu tattauna tunda abinda ya kawoni wajenki kenan" Ina gama faɗar hakan na miƙe jiri na kwasheni na fito tsakar gidansu dan kama ruwa da alwala. Uwani kuma taci gaba da aikin tuwonta, ina kan yin alwala yaran Uwani suka shigo gidan da sallamarsu. Matar gidan buɗar bakinta tace "Wannan wacce iriyar rashin tarbiyyace zaku shigoma mutane gida da gudu, kalan ku zubar mun da miyar da ko kayan ɗakin uwarku in an siyar bazai siya miyar ba?" Yaran su kai turus, ni dama nasan irin matsalolin da Uwani take fuskanta a gidannan shi yasa ban yi mamaki ba, gashi uwani ta kasance kamar zawayi wajen rashin haƙuri ai kuwa nan ta tanka. "Maman Shamsu kenan. Baƙin cikin ki takashinki zai koma da izinin Allah. Ni Uwani nafi ƙarfinki, kuma in mijinki yafi nawa mijin kuɗi, ai ni na fiki more aure tunda mijina bai taɓa zagin iyayena ba. Kuma bai taɓa korata da watan azumin ramadana ba, dan haka ki iya bakin ki" A mugun zafafe Uwani tayi maganar cike da hargowa. Yaran na kaɗa ciki dan gudun kar su kantamo kalmomin da suka shige shekarunsu. Da Uwani da maman Shamsu sun ci uwar sabada har sai da mazajensu suka dawo daga masallaci suka raba wannan ja'iba, dan wallahi na kasa riƙe Uwani sam, har zani Maman Shamsu ta fincike mata ya rage daga ita sai gwari na tsuma ( siket ɗin ciki). Ɗayar matar gidance ta ɗaukoma Uwani zanin ta ɗaura. Baban Shamsu cikin son bin goyen matarshi ba tare da bin ba'asin abinda ya faru ba yace. "A ɗayan biyu ya kamata ko ku ku bar gidannan, ko kuma mu tashi mu bar muku gidan. Wannan bala'in yayi yawa dan watarana wannan jarababbiyar karyar matar taka zata iya illatamun mata'" "Karya kace mata Ƙasimu? Uwani ba karya bace tunda bata leƙen mazan mutane in sun shiga bayan gida. Uwani Iyabo ku shige ciki kar ku tanka musu" Shigewa mu ka yi mu ka barma Hafizu faɗan. Matan gida sai ihu suke yi. Nifa harna rama sallolina ba'a dena gwabza habaice_habaice ba. Wannan ta jefa ma wannan, waccan ta rama, Uwani na tsaye a bakin ƙofa riƙe da labule sai ɓarin zance take ta faman yi. Yara kuma sai cin tuwonsu suke yi a yinwace." Uwani dan Allah ki rabu da Maman Shamsu ki shigo mu tattauna matsaloli" labulen ta saki muka shige uwar ɗakinta duk muka yada zango a kan katifa" Wai Uwani me matarnan take nufi dake ne haka?" "Sharri mana, baƙin ciki take yi mini. Jiya jiya fa na kamata tana barbaɗa mun garin magani a ƙofar ɗakina, kinga ɗauki babu daɗin da mu kaita yi kuwa? Mune har gidan mai unguwa fa. Amman kinga ta sake takaloni" Ajjiyar zuchiya na sauke . Labarin duk matsaloli na ba uwani, da ƙudirina da dalilin zuwana wajenta" "Lallai rayuwar mata cike take da ƙalubale mai tarin yawa. Wata matsalarta uwar miji irinki, wata matsalar ta ƙannen miji, wata jarabawarta maƙotane marasa ƙaunarta irina. Wasu dangin mij, wasu matan maƙota, wata ma abokin mijina, ko matar abokin mijinta sune matsalarta, banda kishiya da shegiya facala su ba'a lissafinsu ma. Na tausaya ma Dada aimun. Kuma ya kamata ku yaranta ku haɗe kai lallai ku nema mata takaddarta. Iyabo amman ramar da kika yi da sauyawarki ta ban tsoro" Hawayena na share. Uwani ƙauyene fa sosai can inda na koma. Babu ruwan famfo, sai wata rijiya guda ɗaya jol anan ake ɗiban ruwa, ba wutar lantarki, babu sabis ɗin waya, ba titi, amman suna da makaranta, sai dai al'ummar cikin ƙauyen aikinsu kenan kiyo, matansu kuma tallar Nono, suna da ƙarancin ilimin addini, ai dole ki ganni haka. Kuma jinya nayi magashiyyan sai an ɗaga sai an ƙwantar" Mun jima muna tattaunawa, sai da mu kai sallar isha mu ka ci abinci sannan Uwani ta zura mayafi muka nufi gidan Hajiya Salamatu. "To naji bayaninku. Amman Uwani kin mata bayanin komai da komai dai ko?" Cewar Hajiya Salamatu tana hakimce taci gwala_gwalai kunne da wuya, da tsintsiyar hannu. "E Hajiya na yi mata bayani. Sai dai itama bata da kuɗi kamar dai ni. Amman Hajiya in muka je can za'a cire a kuɗin aikinmu har mu gama biya. Mu ba ma daɗewa zamu yi a can ba shekara uku ya ishemu, dan da ita Iyabo shekara biyu ma tace" Hajiya tayi dariya tare da girgiza kai. MRS BUKHARI 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundati https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 15 Kafin tace. "Ba dai shekara biyu ba, dan a ƙalla ba a ƙasaru ba, zaku iya kaiwa shekara guda kuna biyan kuɗin jirki da duk abinda aka kashe muku. Sai dai in babban gida kuka samu suke biyanku kuɗi da kyau, amman in ba haka ba shekararnan sai kun yita. Babu rufa_rufa sai kun gama biyan kuɗin jirgi zaku samu damar yin aikin hajji da umara baki ɗaya. Amman muddin kuka zama masu hazaƙa da kazar_kazar to gidan da za'a kaiku aiki zasu soku, kuma in dawowarku najeriya tayi, su hadoku da goma sha tara na arziki." A nan na fahimci Saudiyya zata turamu, sai naji hankalina ya ƙara kwantawa. Kafin mu baro gidannan mata da tsofaffi a ƙalla mutane fin ishirin sai da suka shigo, duk akan batun tafiyar. Ni dai mun tsayar da magana akan gobe da safe in zo mu je hajj kam aimun fasfo kafin in koma garinmu, nan da wata ɗaya da kwana goma jirginmu zai ɗaga zuwa ƙasa mai tsarki. Muna tafe muna ɗan tattaunawa har bus ta saukemu a unguwar su Uwani. Muna sauka muka ci karo da mijin Uwani yana zaune a wata majalisar maza ƴan sa ido. Zumbur ya miƙe da ganinmu ya nufomu gadan_gadan. "Ke Uwani daga ina kike?" Ya faɗa a fusace. Tsaki uwani ta ja tace. "Aikin banza aikin wofi, ka dai ji kunya ka kuma yar da zuchiyarka kare ya cinye. Maza majiya ƙarfi masu zuchiya, ka gansu a titi suna aikin sufuri dan su rufa ma iyalinsu asiri. Banda kai Hafizu baka da aiki sai zaman majalisa, duk matar data wuce kuna ƙarema surarta kallo, ka barni da buga_buga mata a layi duk sun rainani" A faɗace take maganar tana yi tana kumfar baki. Shima zabura yayi ya ce. "Duk macen da take fita dai ba da sanin mijinta ba mala'ikun Allah har taje ta dawo suna tsine mata. Shashasha kawai." Tsaki ta buga fuu ta wuce ta barmu a tsaye. Hafizu ka ƙara haƙuri dan Allah. Dama har yanzu irin wannan zaman na rashin daraja kuke yi ma junanku? Ga yara sai sake girma da mallakar hankali suke. Ko dan su ya kamata ku sarara dan kune allon kwaikwayonsu, kai tunda kaine babba ka dena biye mata" "Shikenan Iyabo. Amman Uwani da kike gani bata da daɗi. Kwananta goma cib tana gaba dani, bansan sam abinda na aikata mata ba. Motsi kaɗan sai habaice_habaice" "Iyabo wai ki zo mu tafi kin kuma tsaya wani lallaɓashi" Ƙwafa tayi ta kawar da kanta. Har muka isa gida tana zazzago mun mita. A falo na kwanta ni da yaran, kafin gari ya waye kuwa suka jiƙani shakab da fitsari sai da nayo wanka kamar mai kwanan turaka dan har kaina sai da ya jiƙe da fitsari. Ai kuwa Uwani ta shiga jibgar yarannan kamar Allah ya aikota, haya_haya tsakaninta da Hafizu bai tsaya ba sai da ya gaji ya bar mata gidan tukunna. Ni na fitar musu da katifar na zuba ruwa katifar ta hau yarari tana gudana a tsakar gidan. Uwani kuma ta wanke musu kayan tas ta goge ledarta tsab da ruwan toka, gabaki ɗaya zarnin ya ɗauke. Dumamen tuwo tayi mana bai ma isaba saini na ba da hamsin aka siyi gasara da siga Uwani ta dama mana. Muna karyawa Hafizu ya leƙo "Ki kawo mun abincina ina tsakar gida" Yana faɗa ya saki labulen tare da jan dogon tsaki. Kai mishi abincin tayi ta dawo muka ƙarashe namu, a gurguje muka fita a gidan bayan ta sallami yara ƴan islamiyya. Ni ko Uwani kin je kin dubo su Toye kuwa?" Ɗan murmushi Uwani tayi tace. "Na yi tunanin Hamma ya goge miki tunanin Gwadabe ne ai Iyabo da baki tambayesu ba" Dariya nayi nace. Ko kusa meye tsakanina da Hamma da har zai ture matsayin uban ƴaƴana a zuchiyata? Shi fa Gwadabe Mijinane, shi ko Hamma ɗan uwanene kuma wa a gareni mai kulawa dani. Uwani kinsan Allah son Gwadabe nunkuwa yake yi a duk ranar duniya, bana jin zan iya sauraren wani da sunan aure a zahirin gaskiya" Ajjiyar zuchiya na sauke take ƙirjina su kai mun nauyi. "Naje kusan sau uku dubo ƴan biyu. Allah cikin ikonshi ban samu ganinsu ba, har shi Gwadaben. Sai da mu kai zageni in zageka da wanna figaggiyar matar wan Gwadabe Haula take ko Zuriya oho" Gabana ya yanke ya faɗi nace. Shikenan duk yanda akayi rayuwar yarannan ta koma ƙauye, ni da naso yaran su samu ilimin zamani tunda ni da Baban nasu iyakarmu kammala sakandare. Yarana sun zama ƴan ƙauye shikenan" Kuka na saka a hanya muna tafe kafin mu samu abun hawa. Da ƙyar da siɗin goshi Uwani ta shawo kaina. Amman fa har muka isa gidan Hajiya Salamatu bana cikin hayyacina, muna zuwa aka kwashemu a golf kusan mu tara zuwa hajj kam, anan muka amsa tambayoyi dai haka bamu jima ba duk yawanmu kuma akwai sanayya sosai tsakaninsu da ita Hajiyar. Muna bakin ƙofar Hajj kam ɗin a tsaye Uwani na kuma tausata wata mota fara sol tayi tsaye a gabanmu, ita bata wuce ba, gashi ta tare mana ganin gari" Wani dattijone baƙi mai haiba da kwarjini ya fito. Saye da yadin boyel mai ruwan ƙasa, kansa saye da hular zanna bukar, ga zobe ga agogo, ga takalminshi sau ciki irin na ƴan gayun maza. Abun almara sai muka ga ya tsaya a gabanmu. Gemu mai shi kombineshon ɗin fari da baƙi na kalla "Assalamu alaikum ƴan mata" Ya furta da muryar kamana muryarshi da kauri irinta tsayayyi dakakkun maza, sai buso ƙamshi yake yi" "Ba dai ƴan mata ba. Ko wacce da yaranta, kuma ai ko da wasa ba mui kama da ƴan mata ba" Cewar uwani balbalin kenan, ni ko fa bance komai ba. Wannan dattijo yayi murmushi har haƙorin makanshi fari ya bayyana. "Allah ya ba manyan mata haƙuri. Dan Allah kuna da aure ne?" Ya tambaya, sai naga fuskarshi ta cika da fargaba. "Ni dai ina da aure. Amman Iyabo a kasuwa take" Sai ya sauke ajjiyar zuchiya tare da murmusawa yace. "Alhamdulillah. To Hajiya in ko babu damuwa inaso mu ɗan yi magana a gurguje, dan gudun kar in katse muku hanzarinku" Carab uwani Tabalbalin tace "Babu komai bari in matsa in baku waje" Ai kuwa sai ta karasa wajen matan da muka zo tare dasu tayi tsaiwarta "Sunana Buhari Namoriki. Nazo shiga Hajj kam ne Allah yasa nai tsuntuwa dake. To a gurguje zanso jin sunanki da unguwarku sai in zo gida in sameki yafi mutunci" Ajjiyar zuchiya na sauke. Idanuna suka cika bam da ruwan hawaye, sai nake jin kamar tsaiwa da wani namiji da sunan soyayya tamfar cin Amanar Gwadabe ne" "Malama Iyabo baki ce komai ba" Na ji sunana raɗau a bakinshi. Sunana Iyabo kamar yadda ƙawata tace. Unguwarmu kuma ni ba ƴar garin bace ma, zuwa nayi gobe zan koma ina mai baka haƙuri" Murmushi yayi yace. "Ai mai son ɗan tsuntsu shi ke binshi da jifa. Kuma garin masoyi baya nisa, in kika bani dama ko adireshi zaki ganni" Ba ko wanne garin na masoyi bane baya nisa. Ka ganni ƴar ƙauye ce a jeji nake rayuwata, babu wutar lantarki balle har sabis ya isa mana, gashi ban shirya aure ba. Wallahi ko zan yi aure bazan auri ƙabilar da zata zama tana ƙin ƙabilar dana fito ba" na ƙarashe zancen cikin rishin kuka. Hajiya Salamatu na hango ta fito, a wajen na tafi na bar Buhari a tsaye. Har motarmu ta fice fit yana tsaye yana ƙarema motarmu kallo. Ko da muka isa gida Uwani Tabalbalin ta balbaleni da faɗa akan me zance ma Buhari haka? Ta tambayeni ne na bata labarin yanda mu ka yi. Uwani ai ni da Bahaushe sai dai zumunci. Amman bazan sake auren Bahaushe ba. Bama yanzu zan yi aure ba kin ganni nan. Mu da muke da tafiyar da zamu yi har tsawon shekaru uku, da dakon soyayya kike son inje inyi wanna shekaru? Dame zanji, da mutuwar aurena, ko da mayar mun da yara ƙauye, ko da matsalar Dada?" Da rishin kuka na masifa nake maganar. Uwani sai ita ta sakko, zama tayi ta dafani. "Kina da gaskiya ƙawata. Amman da ba irin rabuwar da kuka yi ba kenan. Rabuwa salamun_salamun yafi, domin bakasan inda rana zata faɗi ba. Batun yaranki da zan baki shawara ki ɗauka da kin sa ƙafa kin yi fatali da sha'anin, domin yafi ƙarfinki. Ba dole sai sun yi karatun boko darajarsu zata ɗagu ba, akwai arzikin da yafi noma ne? Babu shi da noma yaranki maza zasu iya azurta Iyabo, ita mace aure dama ka iya kaita jeji ma, ki bisu da adda'a zata bisu har gadon baccinsu Gwadabe kuma nasan ya cika jarumi, kuma yayi miki halacci. Amman cireshi a zuchiyarki wajibun ne saki ukune a tsakaninku. Ke ko saki ɗaya yayi miki yaci ki haƙura kema kiyi fatan samu sabuwar rayuwa a gaba. Kawo ɗari a siyo taliyar murji mu ɓararraka ina da maggi da ragowar manja. Kullum aikin kenan nike faɗi tashin neman abun rufin asirinmu, ke Iyabo har wanki da guga inayi a cikin gidannan, yawon wanke_wanke a gidajen masu hali ko shagunan cin abinci har ya zamemun jiki" Ɗari da hamsin na bata dan yara ma in suka dawo sa lasa. Ita da kanta ta fita ta siyo, tare mu kai hidimar komai muka baje a tsakar gida, Maman Shamsu tana zaune a kan turmi tana fige kasa tana waƙoƙin neman masifar da ta saba. A tukunyar muke ci, mun ɗebama yara nasu, Hafizu kuwa nayi roƙon duniya ta dibar mishi Uwani tace bai isa yana zaune a majalisa yana aikin bin matan mutane da ido ta ajjiye mishi abinci ba. "Amman iyaa Debisi da shi kanshi Debisin basu san kin shigo Kano ba?" Sai da na haɗiye taliyata na tsotse yatsuna daya jiƙe da romon da ya ji kafi zabo kafin nace. Babu wanda yasan na shigo. Gobe zan daka sammako in koma. Zanje inci gaba da jiran lokaci in Allah ya kaimu. Kuma inaso in tattauna sosai da Dada ta san ƙudurina, ta goyi bayana akan tafiyar da kuma batun Mahaifin su Baɗɗo. Zan soma zama dasu Boɗɗo tukunna mu tattauna in ji ra'ayinsu. Kuma naso in ɗan dinga ba matan Rugar ilimin addini iyakar abinda na sani, ko dan karatun sallarsu ta yi kyau. To basu ma da lokacin kayinsu ne shine matsalar. Amman su ƴan uwan nawa zan tsaya a kansu kafin in tafi in ɗan gyara rayuwar tasu" Washe gari asubar fari Uwani ta rakani tasha, ta ɗan tsintomun kayanta kala biyu da wanda na sauya a jikina uku kenan. Naso in mata turjiya amman taƙi sam dole haka na karɓa. A tashar na ɗan sai maganin ciwon kai, da maganin ciwon ciki, da maganin zazzaɓi , dana rage zugi ko wanne kati_kati. Inaso in bayar a kaima Dada ta ɗan dinga sha, sauran kuma in ajjiye a wajena. Taran safe motarmu ta ɗaga. Gwadabe:. Takai. Tun a ƙofar gida ya hango motar Yaya Hambali a gefe guda, kuma ya ga Nazifi na zance da Nana ƙanwar Layla. "To Gwadabe ni da Toye zamu wuce gida, in kun gama ganawa da Baba Magaji dasu Babala ka sameni a gida" Cewar Bara'u kenan. "To Shikenan sai nazo. Ka isar da saƙon godiyata ga Sakina" Yana faɗar haka ya shige cikin gidan. Da Nazifi da Nana babu wanda ya kalli Gwadabe balle su gaisheshi. Zumunci ya riga da ya taɓu, ana rikice_rikice a gaban yara suna ji suna gani, sai su taso da raini da rashin ganin girman wanda aka watsar a gaban idanunsu. Wanda ake mutuntawa kuma a gabansu, sai su taso da ganin girmanshi ainun. (Wannan kuskuren namu ne iyaye. Mu guji yin abinda bai dace ba a gaban yaranmu. Shi fa zumunci da haɗin kan haula babu abinda ya kai shi daɗi) Gwadabe yana tafe yana girgiza kai, ciwo yake ji a zuchiyarshi sosai ta yanda zumuncin gidansu ya lalace. A falon Babala ya tarar da kowa da kowa. Babala da nata tawagar haka ma ƙannenta su Goggo Iyatu Baba Magaji yana tsakiya. "Gwadabe kaine tafe da yamma haka?" Cewar Baba magaji. "Nine Baba Magaji. Mun same ku lafiya?" Gwadabe ya bi kowa da gaisuwa Babala da Goggo Iyatu fur su ka ƙi amsawa. Baba Magaji yace. "Zauna nan." Ya nuna mishi kusa da Yaya Hambali. Yana zama Yaya Hambali ya matsa, har yana share sangalalun hannunshi inda jikin Gwadabe ya gogeshi. Da mamaki Gwadabe ya dubeshi, shi kuwa ya zuba mishi Uwar harara. "Marar kunya ji yanda kake ƙare mishi kallo sai kace sa'anka" Cewar Yaya Halima da bata fiye son a zauna lafiya ba dama" Baba Magaji ya yi mata daƙuwa tare da cewa. "Ungo naki Yau ga mutuniyar banza. Shi Hambali baki ga share hannunshi yake yi in da jikin Gwadabe ya goga ba? Sai kace wani karfa. To magana dai ta ƙare kai Gwadabe meye hujjarka na nuna zafin ƙiyayyarka ga ƴar uwarka Laila? Dan naji labarin komai" Gwadabe ya ɗago kanshi yace. "Ba ƙin Laila nake yi ba, face ƙin munanan halayanta abun ƙi. Na farko Laila babu wanda bai san ɓarauniya bace. Ko yanzu a taronnan in ba'ai da gaske ba sai ta raba wani da abunshi. Sannan da aure a kanta bata dena bibiyata tana turo mun da saƙonnin ƙauna ba. Wannan manyan dalilan yasa bazan taɓa iya auren Laila ba" Kafin ya rufe baki Goggo Iyatu da Laila suka fashe da kuka wi_wi. Ganin haka yasa Babala soma shessheƙar kuka itama. Baba Magaji yayi tsam yana bin kowa da ido ɗaya bayan ɗaya yana karantar yanayinsu. Yaya Hambali cikin zafin ranshi yace. "Uwar ƴaƴan naka ma naga ɓarauniyace. Wacce iriyar sata ce bata tabka mana a cikin gidaba? Ai kai kasan komai tunda kai ke biyan kuɗin duk abinda ta sata. Ita ka zauna da'ita sai Laila jininka ce ba zaka iya aura ba?" Gwadabe yace. "Wallahi ko tsinke Iyabo bata taɓa sata ba. Duk wannan kitumurmurar Laila ne. Ita ke satowa ta jefa ma Iyabo a ɗaki. Ni kuma ina biya ne dan ba son ganin ana tashin hankali nake yi ba" "Babu shakka Gwadabe " "Duk ya isheku haka ku saurara mun. Iyatu ku yi mun shiru ya isa haka nan" Sai da ɗakin yayi shiru kana yace. " Duk wannan kumfar bakin da kuke yi ba daidai bane sam. Layla dai kowa yasan mai dogon hannuce, tunda har maraɗi wajena Iyatu ta kawota ai mata magani. A lokacin hekarunta baifi goma ba. Sata kuwa da ta dinga yi a ƙauyannan abun yayi muni. Ina bayan Gwadabe na ƙin amincewa da auren Laila. Tunda kunce satarta shafar aljanune sai ku dage ku nema mata magani. Kuma da ace ni nasan irin tsangwamar iyalin Gwadabe da kuka yi da tuni nayi ma tubkar hanci tuni. Ko yanzu ma dan saki ukune a tsakani da ko kun ƙi ko ku so sai ta dawo tunda itama musulmace ahalul kitabi ma aurensu akeyi ballantana ita musulma gaba da baya." Falon yayi shiru sai hawa da saukar numfarfashi kawai. Baba Magaji yace. "Yaran dasu ta tafi ne Gwadabe?" "A'a Baba Magaji bata tafi da su ba. Shi Toye yana hannun Bara'u Sakina zata ci gaba da kulawa dashi, za'a sa shi a makaranta. Su kuma ƴan biyun na kaisu wajen Tamu a can Abuja shi ya buƙaci hakan" Baba Magaji ya jijjiga kai yace. "To Allah ya saka musu da alheri. Faɗuwa tazo dede da zama ni zan tafi da Gwadabe maradi yaje ga su Auwala can suna aikin haƙar zinariya, yaje shima ya jaraba wata ƙila arzikinshi yana can. Akwai ƙannenka mata ma a cikin gida, in kuka daidaita da ɗaya daga cikinsu kaga sai ayi tuwona maina ku yi zamanku a can. In ma aikin haƙar zinariyar bai maka ba akwai aiyuka da zasu dace da kai" Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke kuma yaji daɗin hukuncin da Baba Magaji ya zartar, shi kanshi yana da buƙatar yin nesa da danginshi ya fita neman na kanshi. Kuma yaji aikin haƙar zinariyar ya kwanta mishi a rai. Ya je can maraɗi ya samu sababbin ƴan uwa da zasu so junansu. Babala ba haka taso taron ya watse ba, amman bata da ikon cewa komai. Haka tana ji tana gani washe gari Gwadabe da Baba Magaji suka wuce maraɗi a bisa jagorancin Bara'u zuwa tashar mota. Wannan shine dalilin barin Gwadabe Kano, ya koma maraɗi hannun wan mahaifin Babala" JIHAR MARAƊI DAKE CIKIN JUMHURIYAR NIJER Cikin unguwar Ali ɗan tsoho. GWADABE:. Bayan saukar su Baba Magaji a abun hawan da suka hau zuwa layin Ali ɗan tsoho. Duk inda Baba Magaji ya sauke kafarshi nan Gwadabe yake ajjiye tashi turyan_turyan har zuwa ƙofar gidan Baba Magaji mai ɗauke da cikowar almajirai yara da ƙananu. Almajiran malam suna hango malam magaji, wasu gardawa biyu suka taso suka nufo su. "Malam maraba da dawowa sannu da zuwa baƙo? Malam baƙin gaddi mu ka yi ne" Baba Magaji yayi Dariya ya dafa wanna gaddi yace. "Ba baƙin gaddi bane. Ɗan wajen ƙaunata ne cikin ummata. Amman da dare zai zauna ya dinga biɗar karatu, da kuma Asuba. A karɓi jakar hannunshi ku shige dasu wajen Fhatsima." Gwadabe ya bi bayan Gaddawannnan biyu har zuwa cikin gida. A tsakar gida suka tarar da matan malam Magaji su hudu reras ko wacce da abinda take yi. Haka yan matan gidan, wannan na sukola, wannan na girkin abincin siyarwa, wannan na dakan fura, duk dai gasunan. "Almu baƙi mu ka yi ne, cewar Baba Fhatsima. Wanda ta kira da suna almu yace. "Malam ne ya tawo da shi ya. Kuma yace mu kawo shi wajenki." Fhatsima ta yi murmushi tace. "Yaro shiga wannan ɗakin ka zauna. Ke I'ne zo ki kai ma baƙo ruwa ya sha" Gwadabe har ƙasa ya durƙusa ya gaishe da matan Kawun nashi. Babu dai yabo babu fallasa suka amsa mishi, cikin su ukun babu wacce ta yi mishi kallon arziki. Baba Fhatsima tace. "Tashi yaro kaji ka shiga daga ciki, za'a kawo maka ruwa" Jakar Baba Magaji ya amsa a hannun Almu da ɗan kunshin kayanshi kala biyu wanda Bara'u ya ƙunshe mishi. Ɗakin ya shige da sallama. Wata budurwa tana kwance a ƙaramin gadon bono ta juya bayanta ta yanda mai shigowa ba zai ga fuskarta ba. Kayinta babu ɗankwali sai baƙin madaiaicin gashi mai walƙiya da yai ma kan nata ado. Ba gashi bane mai yawan daya wuce misali ba. Gashi ne wanda bai ko kai tsakiyan bayanta ba, iyakarshi gaba da kafadunta kaɗan. Gashin dai ya sha gyara sai walwali yake yi. Gwadabe ya ɗauke idanunshi daga kallon gashin ya bi ɗakin da kallo, ɗakin ya sha labule mai ɗawisu zagaye da bangon ɗakin dukka. Ga ɗan katakon kwalliyar labule zagaye da ɗakin, a saman labulen an yi jeren kwanukan sulba ƙananu sai ɗaukar idanu suke yi. Ga gadon bono ga gado mai rumfa maulidi, ko wannne gado ya sha lallausan zanin gado mai geza da heart a tsakiya. Kasan ɗakin kafet ne ja mai kwalliya malale takota ina. A gefen gadon bonon an ajjiye babban tulun ruwa mai fenti, an rufe bakin tulun da faifayi. Ga wasu manyan kumbuna da kwallaye anyi ado dasu, banda wata kwaba mai ƙofofin tangaran ita kuma kwabar an ƙawatata da kwanuka da fileti na tangaran nau'i daban daban. Sallamar da Gwadabe ya ji ne yasa ya nutsu ya dena ƙarema ɗakin kallo. Wata farar doguwar yarinyace ta shigo, hannunta riƙe da kofin sulba mai murfi ƙato. A gabanshi ta dure kofin, ta zauna harda lanƙwashe kafarta kamar mai ɗaukar karatu. "Ga ruwa Yaya ka sha kafin abinci ya nuna sai ka ci" Murmushi Gwadabe yayi mata. "To nagode ƙanwata" Kofin silban ya buɗe ya kafa bakinshi a kofin ruwan ga sanyi, Gwadabe sai da ya sha fin rabin kofinnan kana ya ajjiye ya rufe kofin. "Gidanku Malam ya je, ko kaima almajirci kazo yi?" Ta jefo mishi tambayar, kafin ya bata amsa suka jiyo ana kiranta. "Ine ke dibo fito ku tafi ga musa mai baro yana jiranki" Zumbur ta miƙe ta dubi Gwadabe tace. "Zan fita tallen abinci, amman ba jimawa nake yi ba. In na dawo ma ƙarashe hirarmu" Da idanu Gwadabe ya bita kawai, ta fita cikin hanzari. Tana fita Baba Magaji ya shigo, Baba Fhatsima na biye dashi. A ƙasa Baba Magaji ya zauna, Baba Fhatsima kuma ta zauna a bakin gadon bono. "Fhatsima kin gane ɗana Gwadabe kuwa, ɗan wajen ƙaunata Babala, yaro mai yawan ƙuraje?" Baba Fhatsima tace. "Ohh naji naji, shine haka ya zama babban mutum haka? Oh Gwadabe rabona da saka ga idanuna shekara talatin baya, kana yaro kyatunarka na yawan kawo mana ziyara a lokacin kana goye a bambunta" Gwadabe sai murmushi kawai yake yi yana sinne kanshi ƙasa. Wata budurwace doguwa itama mai jiki ta shigo hannunta da kwanon abinci ta dire mishi a gabanshi. "Wannan Ƙaunarka ce Habi kenan. Ashirin ga wanga wata za'a ɗamra amrensu su bakwai cib. Habi wannan wankine Gwadabe." Gaisheshi Hari tayi da ladabi, ya amsa cike da fara'a, ta saka kai ta fita. "To Fhatsima ga Gwadabe na damƙa amanarshi gareki, ki zame mishi uwa tunda kece babba a cikin gidannan. Rigingimu ne na dangi su kai yawa shine na yanke hukuncin tawo dashi in gameshi da su Auwala suna tafiya haƙan zinariya. Sauran bayanin in kwananki ya zagayo zan zaunar dake mu tattauna. Labulen ɗakin aka ɗaga. Wata baƙar dattijuwa mai zanzana ce tsaye ɗayan hannunta riƙe da faranin silba shaƙe da kwanonin silba a kai. Ɗayan hannun kuma riƙe da labulen ɗakin. Dukkansu suka ɗago suna kallonta. "Abincin ɗakin Yaya zaka ci, ko in kai shi turaka?" Babu yabo babu fallasa tayi maganar. Sai da malam ya girgiza kai, Baba Fhatsima kuma tayi murmushi tace. "In banda abinki kema kinsan ai a turaka zaici. Me zai sa yaci abinci a ɗakina ke da ranarki" Guntun murmushi tayi tace. "To wa ya sani abu a dubu Yaya." "Ki kai mun turakata gani nan zuwa" Malam ya bata amsa da kaurin murya da halamun ɓacin rai tattare da shi. Tana sakin labulen ya miƙe ya fita. Baba Fhatsima tace. "Kaci abincin, sai a nuna maka shashen samarin gidan ko?" "To Baba Nagode " Gwadabe ya bata amsa a dalabce. MRS BUKHARI B4B GIDAN 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundation gidauniyar da muka buɗe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya. Waɗanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE) 300 kacal zasu iya kuɗin karatu *Ƴar uwa ina fatan baki mance da kayan ƙamshin Mrs Bukhari gidan ƙamshi ba ko? Ƴar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ƙamshi. Matso kusa ƴar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ƙamshi ya riƙe miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake saƙawa a tsakankanin kaya. Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ƙamshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata. Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haɗe da turaren fesawa a gashi. Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ƙara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ƙamshin kifi ɗanye. Inada humrori kala_kala. Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ƙamshi. Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ƙamshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ƴar mutan Maiduguri kin samu ƙamshi. ( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai ɗauke da abubuwa huɗu manya kuma a kan kuɗi ƙalilan karki bari garaɓasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)* NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI CE 16 Kwanon da aka ajjiye mishi ya jawo. Tuwon ɓula ya gani da miyar bushasshiyar karkashi. A tsanake ya soma ci, wannan tuwo ya bashi mamaki matuƙa dan a ido bashi da kyan gani, amman a baki akwai daɗi sosai. Zama ya gyara yaci gaba da kantara loma. Wannan budurwar dake kwance a gadon bono ce ta yi miƙa ta tashi zaune tana salati. Wankar tarwaɗace kyakkyawa ma'abociyar siririyar fuska da siririn hanci, laɓɓanta suna da ɗan girma kuma a ɗane suke, haƙorinta biyu manya na gaba a waje suke ko da bakinta a rufe yake. Masu irin wannan haƙorin ana ce musu masu haƙorin zomo. Leɓenta baƙine wukul duk da ya fahimci duk mata da yaran gidan bakinsu duk baƙaƙene kuma kamar wani abun suke yi dan leɓen ya zama haka. Bata da idanu manya ƙanana ne idanunta kamar an huda sakwara, ga gashin ido da yaima idanun rumfa, in ba zaro idanun tayi ba ma baka isa ka ga ƙwayar idanun ba." Ganin Gwadabe a zaune yasa ta rarami mayafi ta rufe jikinta ruf. "Kayi haƙuri bansan kana ciki ba" Ta yi magana muryarta na rawa. A gaggauce ta gaisheshi ta fita. Itama doguwace mai kauri yar duma_duma fatar jikinta luwai_luwai dashi gwanin ban sha'awa, ga mazaunai ɓaka_baƙa. Iyabo ce ta dawo mishi rai, da irin yanda in ta yi walliyar ɗinkin buba da zani take burgeshi, da yanda in ya kallli tudun mazaunanta ta bata yake ɗimaucewa. Ajjiyar zuchiya ya sauke a fili yace. "Ina miki fatan samun namiji lafiyye wanda zai kula dake, ki huta a gidan mijinki irin hutawar da kika rasa a gidana. Allah ka sa jin daɗi da nutsuwa a rayuwar Iyabo ta gaba. " Gabaki ɗaya abincin sai ya fice mishi a kanshi ma, rufe kwanon tuwon yayi ya sha ruwa. Yana zaune ƙwalam wannan basamudiyar budurwar ta sake shigowa dan doguwace ingarma. "Baba tace in ka gama in raka ka shashen samarin gidan ka je ka yi wanka ka huta" Ledar ɗan kayanshi kala biyu ya cacuma ya soke a hammata, baice mata komai ba ya biyo bayanta suka fito. Iyayen gidan basa tsakar gidan, sai tsirarin yara matasa masu wasa kawai. Tiryan_tiryan yana biye da'ita har zuwa wata ƙofa da suka shiga yaga ɗakuna kusan bakwai a jere, da ba haya mara ƙofa sai labulen buhu yana kallosu, sai durom biyu na ruwa, da ƴan butoci, da bokiti. Wani ɗaki ta tura ta shiga. "Bismillahi ka shigo" Bayanta yabi zuwa cikin ɗakin. Katifun yayi ne guda huɗu a jere, sai akwatunan ƙarfe suma guda huɗunne, ginine na jar laka, ba fulasta ba komai, ƙasan ɗakin ma ba daɓe ba komai, rairayin ƙasa ne takota ina sai ƴar tabarma da ke shimfiɗe, saman ɗakin kuma jinka ce, sai ƙwan lantarki guda ɗaya jol. "To bayan gida yana waje, akwai botiki, da ruwa zaka iya watsa ruwa. Lokacin sallah ma yayi sai ka sami malam a waje" "Nagode sosai, sai dai bansan sunanki ba har yanzu." Ya faɗa yana ƴar dariya. "Sunana Hadiza" "Ke yar Ine ce?" Ya tambayeta. "E yarta ce ni" Sallama tayi mishi ta fita. Shi kuma ya shiga kewaye yayi wanka tare da ɗauro alwala. Farin yadi ya saka, wanda ya cire kuma ya saka a botiki ya zuba ruwa, kafin ya fita waje wajen Malam. A ƙofar gidan Malam yai musu limanci. Bayan an idar da sallah almajirai sai suka soma karatu. "Gwadabe ga allo da tawada ka iya rubutu ko?" Sai da Gwadabe ya amshi allo da tawada da alƙalami yace. "E na iya Baba, a can Takai ma makarantar allon mu ka yi, sai dai karatun baiyi zurfi ba, banfi izifi huɗu ba" "Hakane na sani Gwadabe. To yanzu daga farkon izifi huɗun zamu soma. Yau ka bar rubutun kayi muraja'a yau da gobe, jibi kuma sai ka soma rubutun allo. Bana son wasa da karatu. Sannan ka zama jajirtacce sai Allah ya dafa maka. Na sani mahaifiyarka bata da daɗi, iyayenmu kansu sun sha yin kuka da'ita. In banda fitina ta Babala ina ita ina kafewa sai ɗanta ya auri ɓarauniya sabida Allah fa?" Ana cikin haka sai ga su Auwala, da Mammada. Baba Magaji ya gabatar musu da Gwadabe, sannan ya mikashi ga Auwala akan zuwa gobe zai soma fita tare dasu. Su Auwala suka karɓeshi hannu bibbiyu, kuma su kai maraba da shi. Baba Magaji yaranshi maza su rai goma sha ɗaya ne ras. Uku daga ciki sun yi aure, suna cikin gidan tare da iyalansu, tara kuma kowanne yana neman kudi, amman shida a ciki kowanne da budurwarshi da tsayayyar magana. Ukun yarane. Washe gari Gwadabe yabi zugar su Auwala zuwa can garin Ɗan Issa inda anan ya ga dandazon dubban al'umma masu haƙan zinariya. Tun daga nesa dai ya hango tudun laka kawai, sai da suka isa wajen ya ga dubban al'umma. Da rijiyoin haƙon zinariya sama da ɗari. Mammada ne ya ja hannun Gwadabe ya kaishi ga shugaba mai kula da ƴan ƙwadagon wajen ya sanar dashi malam ne yace a kawo shi ya dinga ganin aiki kafin a hankali kuma ya shiga ayari. To Alhamdulillah haka rayuwar Gwadabe taci gaba da tafiya, da safe su hau abun hawa zuwa ɗan Issa, da yamma su dawo gida, su ɗau karatu daga magriba zuwa taran dare, da asuba bayan sun yi sallah kuma zasu yi muraji'a kafin kuma su karya su tafi nema. Duk dabdala a ɗakin Baba Fhatsima Gwadabe yake yinta. Mace mai kawaici da son jama'a kenan. A cikin sati guda da Gwadabe yayi a gidan Baba Magaji, ya fahimci ana buga kishi sosai da sosai tsakanin matan Baba Magaji, yaran ma suna taɓawa dan ko wacce ta jaye yaranta, sun haɗe kawunansu isu_isu. Ko wani abune ya faru da ɗan wani ɗakin, sai aita rurrufewa sai dai in na alkhairi ne, ko dan fahari a fito tsakar gida a faɗeshi. Baba Suwaiba da Amaryar Malam sune suka fi gwabza kishi a tsakankaninsu, kasancewar sunfi Baba Fhatsima da Baba Asshi karancin shekaru, sune Baba Magaji ya aura a baya_baya. Dan Amaryar malam yarinyace da bata wuce shekarun Hadiza ba. Yaranta uku duk maza, sune ƙananu sosai a gidan. Fitinarta tafi ta kowa a cikin matan Baba Magaji, sabida tana ganin ai itace Amarya. Su kuma sauran matan kishinsu yafi tsananta akan Baba Fhatsima da yaran ɗakinta da suka kasance manya, masu jam ragamar komai a gidan. Yaya Tasi'u shine Babban yaron Baba Magaji, babban ɗan kasuwane da yake harkar riɗi da gero, kuma yana kiwon tsuntsaye masu darajar gaske, dangin su ɗawusu, da gigs, da Aku, da dai manyan tsuntsaye na ƙasashe da dama. Kasancewar shine Babba shike ciyar da iyalan gidan baki ɗaya, kuma shi ke yi ma yaran gidan Aure, da duk abinda uba yake yi ma ƴaƴanshi. To kasancewar Yaya Tasi'u ya fito a ɗakin Baba Fhatsima sai yaran ɗakin Baba Fhatsima suka zama yara daban a cikin gidan, yana basu kulawa ta musamman, Baba Fhatsima kullum a cikin shigar daraja take. Kuma matar Yaya Tasi'u mai Suna Badi'a tana yawan yin dabgen kaza ta ciko kwano ta kawo ma Baba Fhatsima. Ko Shi Yaya Tasi'un yasa ayo mata miyar kaji cikin tukunya, sai dai su dinga ci, dan ko abincin ɓarayin bata ci, daga can barayin Yaya Tasi'u ake kawo mata ishasshen lafiyayyen abinci. Ko da Sallah Yaya Tasi'u shi ke ma su malam da iyayen nashi mata layya. To ko akan ragon layyar duk shekara sai an samu yamutsi kan na Baba Fhatsima yafi na saurn matan gidan girma da ƙoshi. Haka dai ake wannan rayuwa a wannan gida. Ranar da Gwadabe ya cika sati guda bayan sun tashi daga karatun dare sai Malam ya zaunar dashi. "Gwadabe banyi maka batun mace bane dama nace bari in bari ka nitsa. To kaga akwai ƴan mata a gidana da yawa, duk da bakwai daga ciki am sa lokacin bikinsu. To shine nace ga Hadiza nan ina ganin kamar tafi sauran yaran hankali kasancewar bazawarace ita. Wata biyar kenan da mutuwar auren nata. A halin yanzu dai bata soma fita zance ba, in dai kana ganin tayi maka sai kayi ƙoƙari ku sasanta kanku. In kuma batayi ba, kar kaji nauyi ka faɗamun wacce tayi ma kai ko wacce tayi ma tana cikin waɗanda za'a aurar ne, zan iya baka ita, shi wancan yayi haƙuri. In kuma dukka basu yi maka ba to Shikenan sai in taya ka da adda'ar Allah ya kawo maka wacce zata zame maka alkhairi. Duk da dai mun soma maganar da Fhatsima, Tasi'u da kanshi sai yayi sha'awar maka Hadiza tunda dukkanku Zaurawane. Amman kaje kayi tunani. Gwadabe take zufa ta keto mishi, zuchiyarshi ta shiga harbawa da ƙarfi. Shi a halinnan da yake ciki na alhini da damuwar rashin Iyabo. Ina shi ina wata soyayya? Ta ina ma zai soma wata soyayya, baya jin akwai wata mace da zai iya bata zuchiyarshi harta samu gurbi. To taya zai kuɓutar da kanshi daga wannan tayi na Baba Magaji? Kuma ko yaya ya nuna baya son ko ɗaya daga cikin yaranshi tabbas bazai ji daɗi ba. Kuma shima nauyi da kunyar Baba Fhatsima zata iya hanashi zaman ƙasar. Gashi har ya soma sakewa, ya soma jin daɗin sabon wajen aikinshi, kuma Alhamdulillah shima harya soma shiga rijiyar tono, duk da yanda akaita tsoratashi, da irin yanda ake samun haɗarin ɗaruruwan mutane su rasa ransu ta dalilin rubtawar ƙasa, amman yasa a ranshi tunda anayi, shima zaiyi in sha Allah sai yayi kuɗi. Tunda yanzu zumuncin ma sai kana da hannu da shuni akeyi da kai. "Gwadabe kar ka damu, na baka sati ɗaya kaje ka yi tunani da kyau. Kuma ka kalli yaran da kyau ka zaɓi ka darje, in yaso shekara mai zuwa sai a haɗa auren naku dana su Mammada ayita ta ƙare. Akwai babban filina gashi can, a cikin filin almajiraina suke wanki, da duk wasu harkoki. To anan zaku zauna dukkanku, Tasi'u zai gina ma kowa ciki da falo_falo" Da haka Gwadabe ya tafi ya bar Baba Magaji akan zasu haɗu nan da sati mai zuwa yaji wacce ya zaɓa. Jikinshi a mace ya shiga cikin gidan. Ɗakin Baba Fhatsima kai tsaye ya shiga. Anan ya tarar da Auwala da Mammada suna zaune da abinci a gabansu, da dukkan halama shi suke jira su ci abinci, dan tun zuwansu suke cin abinci a tare. Hadiza, da Ine suma abincin suke cii daga can kusa da gadonsu na bono. "Yaya Gwadabe ya aikin?" Cewar Ine kenan. Sai da ya gaishe da Baba Fhatsima kana ya amsa Ine. Hadiza ta kalleshi da murmushi a fuskarta tace. "Yaya Gwadabe da safe naje nemanka ɓarayinku ban sameku ba yau kun fita da wuri ko?" "Sa hannu Malam muna ci kana amsa musu tambayoyinsu. In wanna yaranne sai mu kai sha ɗayan dare ba mu ci abinci ba" Dariya duka suka yi, dan Auwala baya wasa da harkar cin abinci. Baba Fhatsima tace. "Ato da gaskiyarshi ai. Maza kuci ku samu ku yi wanka sai ku kwanta. Allah dai ya sama nema albarka." Suna cin abincin ana hira baki ɗayansu a haka dai suka ƙare cin abincin. Sai ga Yaya Tasi'u ya shigo. "Kuna nan ba? Anzo a cinye ma Baba ɗan naman nata ba? Baba Yarannan ya kamata a matso da maganar aurensu, a samu suma su mallaki iyalansu, su dena zuwa suna cinye miki kayan daɗi" Ɗan darawa su ka yi, duk suka miƙe suka gaggaisa, Yaya Tasi'u yace. "Gwadabe ya ciwon jikin? Mammada ya faɗa mun ranar daka shiga rijiyar haƙon zinariya kasa bacci kayi, jikinka yaita ciwo?" Kai Gwadabe ya sosa yace. "Wallahu Yaya Tasi'u ai naji jiki sosai. Amman dai yanzu ina ɗan taɓa aikin, ciwon jikin yana ja baya" "E dama a hankali zai bi jikinka. Kama yi ƙoƙari ni naga jarumtarka sosai, dan wannan aikin bana malalata bane." Baba Fhatsima tace. "Ni kaina na ga juriyarshi sosai. Allah yayi muku albarka dukanku Allah ya baku abinda kuke nema duniya da lahira" Da "Ameen" Suka amsa dukkansu. Hadiza tace. "Yaya maganar kuɗin angon baka bamu ba, kar mu rasa ɗinkin" tsaki Yaya Tasi'u yayi yace. "Ana maganar kayan gado dasu katifa yayi kuɗi. Ku ta ango ma kuke yi ko? To kuje dai wajen Antynku Badi'a zata baku atampopin ta siya muku, dan ni ban bata ko sisi ba. Kunga ni an hutasheni, sai in yima Mamana" Nan suka yi mishi godiya. Baba Fhatsima tace "Ai Babannan ( haka Take kiranshi, kasancewarshi ɗan fari kuma mai sunan Mahaifinta) Babu abunda zamu ce da Badi'a sai dai muce Allah ya saka mata da Alkhairi. Tana yi mun abinda ko su Hadiza iyaka kenan. Yarinyace adala. Ina ma su Auwala fatan Allah yasa yaran da zasu auro mana su kasance masu hankali. Sai kaga zumunci ya sake ƙarfi sosai. Kuma naji daɗin yadda Malam ya yanke hukuncin ware su wadannan yaran a gida daban. Ƙila suma kansu su Sabitu su daure ayi zumuncin duka tare da matansu. Kuma kuyi ƙoƙarin haɗe kawunan yaranku waje guda, kar ku sake a raba muku kan yara. Ni bana jin daɗin irin yanda kowa yake jaye ɗanshi jikinshi kaɗai." Auwala yace. "Tabb ni kuma Baba gani nake yi wannan haɗemu da za'yi waje guda ba zai haifar da ɗa mai ido ba. Sabitu da baya ko iya gaishe da mutane cikin daɗin rai. In fa zai gaishemu kamar zai haɗiyi zuchiya haka yake yi, dan ƙaniyarshi dan yasan kashi zan bashi in baiyi gaisuwar bane. Ni wallahi bana son wannn haɗemun da za'ayi" Yaya Tasi'u yace. "Gaskiya ne za'a iya samun rikici sosai, musamman dag ɓangaren su matan da za'a auro bare. Mun tattauna da Malam sosai akan matalolin da ka iya faruwa. Mum kuma yi magana akan irin nasarorin da zasu iya faruwa. Dan a wannan karon Malam ya shirya ɓatawa da duk wanda ya nemi ƙetare umarnin abinda zai gindaya. I zuwa yanzu ya kamata ace an watsar da duk abinda ya shige, a fuskanci rayuwa. Malam bashi da wani buri daya wuce yaga kan iyakanshi a haɗe. To matsalar Baba Asshi itace zata fi kawo matsala acikin lamarin. Amman Baba shi fa malam so yake filin Ɗan Abhuja dake jikin filin da malam ya bayar a gina, ya siya a faɗaɗa harni da Usman, da Jamilu duk mu koma can, sai ya ware ku kuma daban, muma daban. Ni a matsayina na babba sai in kula dasu baki ɗaya" Cikin damuwa da tunanin rashin yiyuwar haɗin kai ga iyalan Malam Baba Fhatsima tace. "Tab aikin da Malam ya ɗebo babbane sosai. Kuma abun zai yi matuƙar wahala asamu abinda akeso. Sai dai zamui ta adda'a kamar yadda muka kwashe shekaru sama da hamsin muna yi. Malam ya matsantama kanshi da damuwa, da tunanin abinda zai dawo mishi da farin ciki da haɗin kan iyalinshi. Akan ɗan wani dalilin da bai kai an kirashi dalili ba duk wannan abun yaketa faruwa, har waɗanda aka auro a baya_baya suma suka shigo da nasu fitinar. Amman in sha Allah komai zai zo ƙarshe a kwana a tashi" Sun jima sosai anata tattaunawa sai kusan sha ɗaya su kai sallama da Baba Fhatsima, su Auwala suka nufi shashensu, Yaya Tasi'u ma ya nufi nashi ɓarayin. A daren wannan rana Gwadabe ya kasa runtsawa, duk da tarin gajiyar wahalar aikin daya kwaso. Kwakwalwarshi sai hasko mishi hotunan ƴan matan gidan kawai take yi. Da wannan tunani ya wayi safiya, suna kan shirin fita Hadiza ta kawo musu abincin karin kumallo. Kunu ne a jug, sai ɗunamen tuwon ɓula da lafiyayyar miyar kuɓewa ɗanya. Da idanu Gwadabe ya bita bayan ta gaishesu tana shirin ficewa. "Hadiza" Auwala ya kirayi sunanta hakan yasa ta dawo cikin ɗakin. Komanta da sanyi take yi, kuma yanayinta na nuna halamar kunya tsantsa. "Ga kayanmu kala bibbiyu ki wanke mana, Gwadabe bata kuɗin sabulu, ko kai ko Mammada" Gwadabe ne ya zaro sefa ya miƙa mata, tasa hannu ta amsa. Auwala kuma ya bata kayan nasu daya cusa a cikin wando ɗaya. Kafin su dawo Hadiza ta wanke musu kayannan tas, harma ta yi musu kwalima ta haɗa da zannuwan katifunsu du ta wanke. Dama su kan yi ma yayyen nasu hakan lokaci zuwa lokaci. Wanki dama suke yi musu kasancewar su basu da lokacin kansu. Yau samarin gidan a mugun gajiye suka shigo sharkab_sharkab da zufa, hakanne ma yasa basu shigarma Baba Fhatsima ɗaki a haka ba suka nufi shashensu. Anan suka tarar da sabitu yana kutuntumama Hadiza zagi tare da faɗin kalma marar daɗi a kanta. "Ƴar iska dama naji labarin ƙazamin kishine irinna gado yasa aka sakoki ai. Dama yaushe zaku iya zaman aure, yara an sangartaku, an ɗaure muku ƙugu, an ɗauraku akan bigiren kishi" Karab a kunnen su Gwadabe. Sabitu na ganinsu yazo da sauri zai wuce, Auwala yayi zafin naman riko hannunshi ya fincikoshi ya dawo gabanshi. "Ai ba ka zazzageta ka tafi a kyauta ba. Dan Allah sai munje gaban Malam yaji duk abinda ya haɗaku har ka zaɓi cin zarafin mahaifiyarmu da shi kanshi Malam ɗin. Kai dai Sabitu baka ƙaunar buɗe idanu ka ga muna rayuwa kyakkyawa. Wannan ciwon hassadar ne ya hanaka ci gaba sam, kuma gashi munfi ƙarfinka nesa ba kusa ba. Hadiza wuce muje gaban Malam. Da ƙarfin damtse Auwala ya figi Sabitu suka ratso tsakar gidan iyayen nasu, duk suna baje a tsakar gida suna shan iska. Baba Asshi taga Auwala riƙe cab da Sabitu, ba shiri ta cire hannunta a cikin abincin da take ci ta bi bayansu har da gudunta, daga ita sai fallen zani babu ko ɗan dires a jikinta. Baba Fhatsima ganin harda Hadiza aka fita yasa itama ta miƙe ta rufa musu baya." Anan na kawo ƙarshen free page. Wasa farin girki, labarin yana da tsawo ainun, dan ba mui komai ba. Sannan akwai tarin rikita_rikita da abubbuwa da dama na darasi, kar ki yi sake ayi wannan tafiyar babu ke. Akwai tarin abubbuwa da zasu biyo baya. Sannan akwai kyautuka da zan rabama masu yin dogon sharhi na musamman. Ki biya kuɗinki kisha karatu. Wasu suna roƙon in buɗe VIP To 1000 ne VIP ɗin normal group 500 ne. Nagode sosai da soyayya Nagode nice taku a kullum Mrs Bukhari. Mu haɗu a paid group dan jin yanda zata kasance. +22785548912 Ƴan Nijar ga number da zaku turama da kati nan nera 500 a kuɗinmu na najeriya. Nagode 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundation gidauniyar da muka buɗe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya. Waɗanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE) 300 kacal zasu iya kuɗin karatu *Ƴar uwa ina fatan baki mance da kayan ƙamshin Mrs Bukhari gidan ƙamshi ba ko? Ƴar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ƙamshi. Matso kusa ƴar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ƙamshi ya riƙe miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake saƙawa a tsakankanin kaya. Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ƙamshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata. Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haɗe da turaren fesawa a gashi. Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ƙara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ƙamshin kifi ɗanye. Inada humrori kala_kala. Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ƙamshi. Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ƙamshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ƴar mutan Maiduguri kin samu ƙamshi. ( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai ɗauke da abubuwa huɗu manya kuma a kan kuɗi ƙalilan karki bari garaɓasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)* NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE LITTAFI NA BIYU 1 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* Iyabo Motarmu na dira a tsaha idanuna su kai tozali da kyakkyawar fuskar Yaya Hamma. Yana jingine a jikin wata Bus ya ƙurama motarmu idanu bai ƙibtaba, bai kawar da kanshi daidai da na sakan guda ba, har sai da yaga na fito a cikin motar. Da sauri ya nufoni fuskarshi ɗauke da yalwataccen murmushi, murnarshi ta kasa ɓuya. Yasa hannu ya karɓi ledar kayana. "Jabu tunda na shigo tasharnan zuchiyata bata dena dokawa ba har sai da na ga sakkowarki a cikin motarnan. Wata zuchiyarma ce mun take yi baza ki dawo garemu ba kwata_kwata" Ɗan murmusawa nayi kawai nace. Yaya Hamma kenan, na gode da kulawa, amman kafin ma in tafi na sanar maka zan dawo." A jere muka fito daga cikin tashar, a bakin titi muka samu motar Girai muka shiga, wata kwaraɓaɓɓiyar Bus mara gudu muka samu. Bayan tafiyarmu ta ɗan yi nisa sai nace dashi. Ni ko ya jikin Dada Yaya Hamma?" Wannan tambaya tawa farad ɗaya saita sauya fuskarshi, daga farin ciki izuwa ɗaurewar fuska, harma da alhini. Lamarin daya dagula jinin jikina kenan, ruɗewar da nayi da yawa ne yasa yace dani. "Ki kwantar da hankalinki Jabu. Bawa baya iya tsara ma kanshi yadda zai rayu. Nayi imani da hakan na faruwa Al'umma babu mai zubar da hawaye. Bayan tafiyarki abubbuwa manya sun faffaru marasa daɗin labari. Amman bazan baki labarin komai a cikin motar haya ba. Kiyi haƙuri in mun je gida zaki ji komai" Bai daina rarrashina ba har muka iso Girai. Ni dai ko da muka shiga akori kura bana iya ko magana sai fargaba da nake cikinta. Jikina sai bani yake yi Dada ta haɗiyi zuchiya ta mutu ne ƙila bayan tafiyata, ko kuma maƙetacin mijinta ya kasheta. Da waɗannan tunane_tunanen muka shiga cikin Jaɓɓi lamba. Sai gamuwa da mata masu tallar nono muke yi Yaya Hamma gidan su Dada zaka kaini, zan tsaya a ƙofar gida sai kai ka shiga" Ƙuramun idanu yayi, sai naji idanun nashi sun yi mun kaifi ba shiri nayi ƙasa da nawa idon, tare da sauraren amsar da zai bani. "Dada bata gidanta, tana gidan Baffa Musa, ki bini kawai in kai ki" Ai jin haka yasa na kuma tsurewa har hawaye sai da ya zubo a idona. Tafiya muke babu mai cewa da ɗan uwansa ci kanka har muka isa gidan Baffa Musa, tafiyar ƙafa ce mai mugun nisan gaske. A ƙofar shiga gidan naci karo da Burodami Debisi shi da Jatau. Sai nayi turus ina dubanshi cike da maɗaukakin mamaki. Shi kuma cikin sanyi yake kallona irin kallon da naso in samu irinshi daga gareshi a shekarun da suka shuɗe, shekarun da wutar sonshi ta kusan ƙone mun rayuwata. Sai a yanzu da bana buƙatar kowa a cikin rayuwata ne, zai dinga jifana da irin wannan kallon? Ko zan iya ba maza wata damar, babu Burodami Debisi a cikinsu, zaifi mutumci ya riƙe matsayinshi na wa gareni "Iyabu Ekabo ( Sannu da Zuwa) Burodami Debisi yaushe a gari?" Na tambayeshi da yaren hausa, babu yabo babu fallasa a fuskata. Jatau yace. "Ai tun ranar da kika yi tafiya shima ranar yazo. Tare muke ta zuwa kiwon shanu" Da mamaki na dubeshi, kuma na yaba ƙoƙarinshi daya iya har kwana biyu a ƙauyenmu. "Mu je ciki Jabu, ki ga halin da Dada take ciki, naga kamar kin sha'afa" Cewar Yaya Hamma da muryarshi a kausashe har ɗan rawa take. Wucewa nayi cikin gidan, Yaya Hamma na biye dani a baya, su Burodami Debisi na biye dashi har zuwa cikin bukkar Goggo matar Baffa Musa. A kwance na tarar da Dada kanta naɗe da bandeji, sai kuma hannun damanta dana ga an ƙulle da tsumma, ga kara an jera mata kamar mai karaya. Sai numfarfashi take fitarwa, Boɗɗo na gefenta a zaune, su Yusufu, da Cubu duk suna kewaye da'ita, harda yaran Baffa Musa waɗanda suke gidan miji, Yafendonmu Jabu, da Yafendo kaɓoji mahaifiyar su Yaya Hamma, da Yafendo A'i suna wajen duka. Kuka kawai na fashe dashi domin na rasa ma abinda zance, bansan wa zan tambaya ya bani amsa ba, kowa a cikin damuwa yake. Boɗɗo ce ta dawo kusa daf dani ta riƙe hannayena biyu. Meke faruwa da Dada Boɗɗo, naga hannunta kamar karayace ma?" Baffa Musa ne yace. "Abinda ya faru kusan sanadiyyarki ne Jabu. Wannan ƙiyayyar da mijin Daso yake yi miki abune daɗaɗɗe sosai. Kuskuren da ita Daso tayi shine data yarda da sharaɗinshi kafin ya aureta. A lokacin da mahaifinmu Allah ya jiƙan rai ya matsa ma da Daso kan a cikin gwarazan samarin da suke neman aurenta za'a saka shaɗi, a lokacin shaɗi gwarazan mazan fulani suke yi su auri mace, dole sai namiji ya nuna jarumtarshi. Aka saka ranar shaɗi, Allah cikin ikonshi sai mai nagge yai nasarar cinye wannan gasa ta neman auren Daso. Gashi matashi mai dukiya, dan Allah ya albarkaceshi da tarin shanu a lokacin. Amman mutumne shi mai zuchiya da kafiya akan ra'ayinshi ko mai muninshi. Duk da wannan kusan ɗabi'ace dake gudana a jinin ko wanne bafulatani, amman na mai nagge yayi yawa. Bayan anyi aure kafin ta tare sai yake sanar mata shi mutumne mai tsananin kishi shi baya son ya saka ɗiyarta ƴar margayi a idanunshi sam, ta yi mai alƙawarin zata kiyaye mishi hakan, amman bazai hanata zuwa ganinki ba, bai kuma yarda yaranshi suyi zumunci dake ba. Ita kuma Daso cikin rashin sanin girman furucinshi sai ta amince mishi da duk abinda ya gindaya. Duk da dai ba'a musu dashi. Jabu daga ranar da yar mahaifnki Toyosi ta ɗakkoki ta kawoki garinnan dan kiga dangin mahaifiyarki, bayan tafiyarku sai da igiyar auren Daso ya kutsure, ta fuskanci tashin hankali, da faɗa sosai harda duka ma a wajen mai Nagge kafin ya korota gida. To shekaran jiya kinje mishi gida, a gabanku ke da Daso ya fashe mata kai. Bayan ya rakaku da gudu sai ya rufeta da duka. Ana cikin wannan hali ranar ko tallar Nono ta kasa zuwa. Sai ga Debisi shima da yamma lis. Zuwanshi ne yai silar da kika ga Daso a kwance tana jinya. Hamma gashi shi yaita kai kawo akan nema mata lafiyarta. Debisi kuma da Jatau suka kaita asibitin Girai aka duba lafiyarta. Wai hawan jinine ma da'ita a yanda su suka ce. Kinji abunda ya faru, amman kuyi hakuri wata rana fa sai labari, masu ba da labarin ma wata rana basu. Haka zamu shuɗe kamar yadda magabatanmu suka shuɗe. Kuka mai taɓa zuchiya na fashe dashi kawai. Wannan zalunci da mai yayi kama, yama za'ayo a raba uwa da ɗiyarta ɗiyar ma ta fari marainiya bugu da ƙari. Tsit ɗakinnan yayi bakwa jin komai sai sautin kukanmu ni da ƙannena da suka kewayeni suna rarrashina. "Jabu ki dena wannan kukan. Ki yafe mini kinji? Yarintace tasa bansan girman sharaɗin da mai nagge ya gindayamun ba, ba dan bana sonki bane na amince mishi ba. A cikin yarana kab nafi jinki fiye da kowa, kasancewarki marainiyar yarinyar da bata taso a gaban mahaifanta ba. Bugu da ƙari soyayyar Toye kanki ta koma kacokam." Hannunta nayi carab na kama, idanu ta lumshe wasu hawayen nadama suka gangaro mata. Mayafina nasa na goge mata. Baffa Musa ne yace. "Daso baki da lafiya bai kamata ki yawaita magana ba. Hutu kike buƙata. Na faɗa ma Jabu wannan labarinne domun tasan abinda ke gudana, ba dan in tashi hankalinki ba. Kai kuma Debisi duk sanda zaka zo wajen Jabu, ka sameta a gidan Yafendonta, ka sanarma Toyosi itama. Jabu ku tashi ku koma can gidan Yafendonku, ki samu ki huta" Ba haka naso ba, so nayi su barni in yi ma Dada jinya. Amman Baffa Musa yaƙi fur sai cewa yayi ma dinga zuwa dubata, matanshi zasu kula da'ita. Muna tafe a hanya amman tunani ya cika kaina, damuwa tayi ma zuchiyata yawa, ina neman wanda zan kwanta a kafaɗarshi in ci kuka ko zan samu salama. Gwadabe ne ya faɗo mun, tunashi kawai da nayi wallahi sai na tsinci kaina ina murmushi kawai. Tare duka muka shiga gida. Ni da su Daso wacce tunda na dawo naga ta fita sha'anina. bukkarmu muka shiga, na nemi waje na zauna jigum. Yaya Hamma ne ya shigo hannunshi riƙe da kayana. Yana shigowa sai naji Daso ta sau siririn tsakin da ba kowa ne zai ji ba. "Ga kayanki Jabu. Ku kuma ku bamu waje zan yi Magana da Jabu" Su Cubu duk suka miƙe suka fita, banda Daso wacce kwanciya take shirin yi. Sai da ya yareta kuma da faɗa naga yana magana. Kuka kawai naga Daso ta fashe dashi ta fice fuu. Ni dai ba ta fishin Daso ma nake ba, ta kaina nake yi. Zama yayi a ƙasa yana fuskantata. Idanu ya zubamun yaƙi cewa dani komai, yaƙi kuma ya dena kallona. Ni kuma duk sai na tsargu. Jatau ne ya leƙo. "Jabu ki zo Debisi yana son zaku yi Magana, yana gindin bishiya, ki je da tabarma, ga fura Hari ta dama sai ki tafi mishi dashi" To" kawai na iya cewa, ya saki asabarin yayi tafiyarshi. Yaya Hamma kuma naga yayi ƙasa da kanshi kawai yana wasa da layar dake ɗaure a tsintsiyar hannunshi" Yaya Hamma bari in je in dawo, tunda naga kamar baka son yin maganar da kace zamu yi" Ɗagowar da zaiyi sai naga idanunshi sun rine, jijiyoyin fuskarshi sun yi burɗun_burɗun. Gabana ya yanke ya faɗi ganin yanda cikin ƙanƙanin lokaci na ganshi a cikin wani irin yanayi. Cikin kaurin murya mai cike da karaya yace. "Shikenan gobe zan dawo, nima zanje gida in kwanta jiri nake ji" Haka kurum sai banji daɗin ganin shi a sabon kamanni ba. Kafin in gama tubkewa ya fice bankai ga warwarewa ba. Jikina a mace na fito tsakar gidan. Tabarma da damammiya fura Hari ta miƙo mun nasa hannu na karɓa. Har na kai ƙofar fita na juyo na kalli Boɗɗo nace. Boɗɗo ku jirani in je in dawo. Inaso zamu je gidanki akwai muhimmiyar maganar da nake son mu tauna" Ina faɗan haka sai naga Daso ta zare idanunta, firgici ya bayyana karara a fuskarta" Ficewa nayi waje. A tsaye a gindin bishiya na hango Debisi yana kallon garken shanun da suke wucewa. Kurama juna idanu muka yi, ina daga tsallake ina jiran shanun su gama wucewa" Zuchiyata ce naji tana bugawa da ƙarfi, idanun Debisi naji sunyi mun kaifi. Na so Debisi so na haƙiƙa, soyayyarshi ta wahalar da rayuwata, dan zuchiyata bata iya son abu ba, in zata so abu da gaske take sonshi, haka kuma ban iya ƙin mutum ba" Bamu dena kallon ƙudan da muke ma juna ba har sai da garken shanunnan suka gama wucewa. A hankali na isa ƙarƙashin bishiyar. Carab ya amshe ƙwaryar damammiyar furar dake hannuna. Na shimfiɗa tabarmar dana fito da'ita, tare da cewa. Bismillahi Buradomi ka zauna" Murmushi yayi mun, irin wanda ada nake mafarkin ganin yanai mun. Banda a yanzu dan tuƙuƙi naji zuchiyata nayi mun. Kuma ina fatan ba cewa zaiyi sona yake yi ba, dan zan iya zaginshi tsab, laifinshi mai girmane a gareni, babu abinda zai iya faɗamun in yarda ba yaudara bace" Waje na samu na zauna kamar yadda yai mun izini. Shiru ne ya biyo baya na tsawon minti shida kafin yace "Bansan ta inda zan soma ba Iyabo. Gashi zuwan nawa ya haifar da matsala mai girma, ina mai neman gafararku baki ɗaya. Amman kafinnan me kika je yi a Kano, sannan wannan ramar duk ta rabuwa da Gwadaben ce, ko kuna cikin wata damuwane?" A jijjere yayi mun tambayoyin da na yi jim, ina cinka cinkar wanda zan sona amsawa a cikin zuchiyata. Sai na sake jin amon muryarshi yana cewa "Da zan baki shawara, da nace ki shirya ki bini mu koma Kano. Tunda kika baro Kano kika barmu cikin kewa da alhinin rashinki. Nawa kuwa yafi na kowa. Kuma a kwana biyu kacal da nayi a rugarnan na tabbatarma kaina rayuwarki ba zata taɓa yi miki daɗi ba. Ke da kika taso a maraya, ga hasken lantarki, ga ruwan famfo, ga makarantu, ga titina, ga_ga_ga. Amman anan fa babu abunda suka sani sai kiwo da tallar nono, ace kamar Dada tallar Nono itama take zuwa yi, su Ɓodɗo ma tallar suke ɗauka fa" katseshi nayi ta hanyar cewa. Tambayarka ta farko gareni shine. Naje Kano ne nayi fasfo zan tafi ƙasa mai tsarki da izinin Allah neman kuɗi. Tambaya ta biyu kuma. Ciwo nayi mai tsayi shi yasa na rame. Gwadabe kuma yana ɗamfare a raina tsaiwar numfashinane kaɗai ka iya kawo ƙarshen soyayyar Gwadabe. Batun rashin iya zaman rugarnan kuma. Zan iya ko dan Dada, da ƙannena. Bana jin komai na dangane da kewar birni, ko ƙyale_ƙyalen dake cikinta. Ni babu abinda a halin yanzu yake burgeni. Nafi samun nutsuwa a haka" Ashe ni na kasheshi da namaki ban sani ba. Sai da na juyo naga bakinshi a hangame yana kallona, da halama ya ɗan jima yana kallon nawa "Saudiyya fa kika ce zaki je neman kuɗi Iyabo?" Ya faɗa a ƙagauce da son jin amsata. E Saudiyya da izinin Allah, Lokaci kawai zamu jira." " Da izinin wa zaki tafi Iyabo, me yasa Kano bata isheki neman kuɗi ba har sai kin dangana da ƙasa mai tsarki, sannan me yasa baki yi tunanin Aure, ko komawa makaranta wanda nasan yana daga cikin burukanki na rrayuwa ba?" Ya sake jejjero mun wannan tambayoyi cikin ɓacin rai a wannan karon. Baki na tsuke bance mishi komai ba. Tsawa ya daka mun wacce tasa ƴan hanjina kaɗawa. "Ba dake nake yi ba kin mun banza ba?" To ni kam Burodami me zance maka? A halin yanzu babu wani karatu, ko aure a gabana. Rayuwar mahaifiyata kawai nake dubawa, da mafarkin samar mata da sauƙin rayuwa. Ka dai taya ni da adda'a zaifi. Dan babu makawa zanyi tafiyarnan. In kaga banje ba Allah ne baiyi ba. Kayi haƙuri kar kace na bijire maka" Sai yayi shiru na wasu daƙiƙu kana yace. "Amman ba kya ganin in kika tsallake ƙasarki Najeriya, kika tafi wata ƙasar neman kudi. Ba kya ganin wasu zasu yi miki kallon da bai dace ba? Ballantana kinga ke bazawarace kina da ƴaƴa. Acan kuma baki san hannun waɗanda zaki faɗa ba" Hannu na gari zan faɗa da izinin Allah. Kuma wama zai san na tafi Burodami Debisi?. Kaga Dada tana cikin halin da ya kamata a taimaka mata. Kuma ni bazan wuce shekara uku ba zan dawo. Kafin in dawo amman sai na tabbatar da na samu dukkan abunda naje nema." Ajjiyar zuchiya ya sauke, yayi shiru yana kallona, ni kuma nayi ƙasa da kaina. "To batun aurenmu sai kin dawo za'ayi kenan. Ko kuwa zaki amince a ɗaura kafin ki tafi? Dan ni harna sanarma Baffa Musa sababin zuwan nawa. Yayi murna matuƙa da jin hakan" Wani kallo nayi mishi, wanda ko a mafarki banyi tunanin akwai ranar da zata zo da zan yi mishi wannan kallo ba. Aure a tsakaninnu babu shi har gaba da abada. Har gobe nice Iyabo mai ƙibarnan, wannan wacce sai da ka kwanta jinyar ƙiyayyarta. In ma mafarki kake yi ka farka" Ina dasa aya sai kawai na miƙe hawaye fal Idanuna. Takalmaa nake shirin sawa yayi maza ya miƙe shina. "Iyabo" Ya kirani da sauri. Cak na tsaya. Ban tafi ba, ban kuma juyo ba. Ina jiyo takunshi har izuwa daf dani. "Nasan kina sona Iyabo kar ki soma yaudarar zuchiyarki. A rashinane kika auri Gwadabe. Iyabo zan baki farin ciki irin wanda mafarki da hasashe ba zasu iya hasko miki ba. Duk duniya ba wanda zai soki sama dani, sai dai ya biyo bayana." Hawayena na share, tare da lumshe idanuna, zuchiyata kuwa sai aikin turiri take. Da ƙyar na haɗiyi miyau nace. Iyabonnance dai wannan mai ƙibar da kaƙi aurenta sabida wannan halitta tata. Ba canjawa nayi ba. Duk da nasan na zabge rabi da kwatan ƙibata, a sanadiyyar halin yau da gobe Ka sani kibata zata iya nunkuwa da kaso sama da hamsin akan na da wanda ka guje ni dominta. Debisi ina mugun girmamaka ne ma yasa harna tsaya saurarenka. Amman da ba dan haka ba ko kusa dani baka isa kazo ba. Maganar soyayya ko aure babu ita, dalilin da yasa ka barni ina budurwa. Dalilin ne dai yasa na barka bayan na zama bazawara" Ina dasa aya nayi shigewata cikin gidan. Duk a tsakar gida na tarar dasu, amman banda Daso. "Adda Jabu Yaya Debisi ya kawo miki wata ƙatuwar leda, tana wajen Adda Daso. Muma duk yayo mana tsaraba mai yawa" Ɗan murmushi na ƙaƙaro nace. Ayya. Ai Burodami Debisi ba daga nan ba ta wajen kyauta. Boɗɗo ku taso muje gidanki, dan acan nake son mu tattauna kamar yadda na faɗa miki ina da Magana da zamu tattauna daku. Ina zuwa bari in samu Daso in sanar mata" A cikin bukkarmu na sameta tayi tagumi sai aikin tunani take faman yi, dan bata san ma na shigo ba har sai da nazo daf da'ita. Ta ɗago fararen idanunta ta zuba mun su. Akwai damuwa sosai a tattare da'ita, wanda a tunanina baya rasa nasaba da kewar tsohon mijinta marigayi. Daso wai me ke damunki ne, ni tunda na dawo na ganki wani sukuku. Ko duk rashin lafiyar Dada ne?" Na jefeta da tambaya, tare da kafeta da idanu domin karantar yanayinta. "Ba komai abubbuwane sukai ma zuchiyata nauyi Jabu. Amman zamu tattauna zuwa dare" kai na gyaɗa mata kawai. To ni zanje gidan Ɓoɗɗo akwai maganar da zamu yi dasu duka" Kur ta mun da idanunta kamar mai karantar wani abun a fuskata, sai kuma ta ja numfashi tace. "Bari in zo muje, inaso dama inje wajen Hama, in yaso in kun gana tattaunawar sai ki same ni a ɗakinta" Hakan ko akayi, a hanya ne take labartamun Debisi ya kawo mun wata ƙatuwar leda, ta adana mun ita. Ni dai kai kawai na gyaɗa. Mun ci tafiya sosai kafin muka iso gidan. Matan gidan duk suna tsakar gida anata tuwon dare, wasu kuma suna wanke ƙoren tallar nononsu, Yafendnmu bata nan bata dawo daga can gidan Baffa Musa ba. Daso ta ya da burki a ƙofar bukkar Hama, tana zaune tana tuƙin tuwon masara, masararnan fara tas gwanin ban sha'awa. Da dariya da haba_haba muka kaisa da Hama kafin muka shige bukkar Boɗɗo. Bayan kowa ya nemi waje ya zauna, sai na yi gyaran murya na soma da cewa." Dukkanku kun fini sanin irin halin da Dada take ciki a gidan aurenta. Da irin matsalolin duka, da tsangwamar da Baffa yake yi mata. Ku yi haƙuri Baffa mahaifinku ne, amman nasan ku kan ku kunsan yana zaluntar Dada. A shekaru irin na Dada ai yaci ace ko da an daketa a baya, a yanzu a barta ta huta ko dan kaifin idanunku. Ga yawon talla, duk rauni da da gajiyar dake jikinta tana talle. Amman anan naga ku kamar talla wani abune na dole." Boɗɗo ta tari numfashina da cewa. "Talla tana cikin sharaɗin aurenmu mu kam. Domin da kuɗin nononnan zaki ɗauke nauyin ci da sha na gidanki, harma ki yi ma kan ki sutura da dukkan buƙatu. Su kuma maza aka barsu da kiwo. Sai dai wasu matanma suna fita kiwon su dawo lafiya. Dukan da Baffa yake ma Dada ni shine damuwata. Anan ɗakin mun sha zama domin tattauna wannan matsalar, rashin mafita ke sa mu yi haƙuri kawai. Amman zukatanmu na sosuwa ainun, hakan ya zabtare kima da darajar Baffa ta Uba a garemu. Domin mun fi son Dada sama dashi sai dubu babu haɗi" To ni dai ina da shawara, so nake zan tafi saudiyya neman kuɗi. In na tara kuɗi zan dawo, inaso Baffa ya saki Dada ne kawai. Ni kuma zan ɗauketa harda su Yusufu in sai mata gid, ta zauna ta ci moriyar haihuwa ko wanke_wanke ni zan dinga yi mata ko da nayi aure. Amman meye shawararku kune ƴan uwana?" Boɗɗo tace. "Da hakan zai faru wallahi Adda sai mun fi kowa farin cikin faruwar hakan. Ni da Amaduyal mu muka san irin wuya da dukan da Baffa ya dinga yi ma Dada. Har ɗaureta yake yi a jikin gadonta ya daketa ciki da waje." Anan suka sake fayyace mun halin da Dada take ciki a gidan aurenta. Kuma duk suka bani haɗin kai akan suma sun amince a saki Dada. Sai dai wani hanzari ba gudu ba, duk yawan shanayen Dada dake hannun Baffa bazai yarda ya bayar ba. Ni kuma a wannan lokacin sakin kawai nake buƙata ba shanayen banza ba. Sai da mu kai sallar isha a gidan. A ɗakin Yafendo muka haɗu mu ka ci abinci anata hira, maza kuma suna waje suna shan iska. "Cubu je ki kira Hamma a waje ya raka su Daso guda, kuma sai ku kama hanya tunda ga Yusufu sai yai muku jagora" fitar Cubu ke da wuya sai gata Yaya Hamma na biye da'ita. "Dada gani" Ya faɗa da murya mai kauri. Yarinyarshi dake hannun uwarshi sai ɗaga mishi hannayenta take yi halamar ya dauketa Hama ta miƙa mishi yarinyar ya ratayeta a kafaɗarshi. "Su Daso zaka raka gida tunda dare yayi ." Ɗan murmushi yayi kawai kafin yace. "To Dada su sameni a waje sai mu je. " A tsaye ya ɗan yi ma ƴar tashi wasa ya miƙa ta hannun uwarta ya fita. Muma mu kai ma Yafendo sallama muka fito, suma su Yusufu suka nufi hanyar komawa gida. Shiru_shiru mukaita tafiyar. Duk cikin mu ukun kowa da abinda ke azalzalar zuchiyarshi. Abun mamaki har muka isa gida ba wanda yayi ko tari. A ƙofar gidan muka haɗu da Jatau da Burodami Debisi sun kafa sun tsare suna jiranmu. "" Ƴar halak ta ƙi ambato ka ganta ma. Jabu mun fi mintu talatin muna jiranki anan wajen" Hannu Yaya Hamma ya miƙa musu suka gaggaisa, sai naga ya kuma haɗe ranshi. Ni da Daso dai muna tsaye, Allah cikin ikonshi sai ga Manga shima ya tawo taɗi shi da abokinshi. Yaya Hamma ne yai ma Daso jan ido ta je wajensu. "Jabu ki je ki saurareshi, ni zan jiraki a wancan wajen itaciyar, inason mu yi magana ne" Yaya Hamma ya faɗa a sanyaye. To Yaya Hamma" Iyakar abinda na faɗa kenan. Burodami Debisi yaima Hamma godiya, ni dai na bi bayanshi dai muka matsa gefe haka. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI CE Ina miƙa saƙon gaisuwa ga masoyana. Sister Khadija maidoki ina godiya. NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE LITTAFI NA BIYU 2 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* "Gimbiya Iyabo sai wahalar da zuchiyata sonki yake ta yi. Ni na ɗauka dake zan koma Kano a matsayin matata fa, ashe abun ba haka bane. Ki tausayama masoyinki ki tsamoni daga cikin halin da kika sanyani, kaina bisa wuya, banda tuno baya. Kuma nayi imanin su Iyaa da Burodami kokodeen zasu yi alfahari da aurenmu Iyabo " Duk wannan maganar yana yinta ne cikin kyakkyawan lafazi mai taushi. Maganganunshi babu inda basa ratsawa a jikina. Sai dai kash ya makaro, dan banga abinda zai iya cemun in yarda dashi ba. Ina Mai baka hakuri ka fitar dani a zuchiyarka dan Allah. Nayi imanin a rashin samun yadda kake so a wajen matarka soja ne yasa kake son ni ka aureni" Da sauri ya fuskanceni sosai cikin kidima yace. "Wallahi bazan iya ba. Baki san irin azabtuwar da ruhina da gangar jikina suke yi bane shi yasa. Ki dena tunanin dan ban samu yadda nake so a wajen Yemisi bane na dawo gareki. Iyabo ina sonki" Ɗan guntun murmushine ya sufce mun ba tare da na shirya ma hakan ba. Zaka iya, tunda har na iya cire sonka a zuchiyata. Na rungumi soyayyar Gwadabe har kuma ya samu matsayin da babu wani ɗa namiji da zan iya bashi wannan matsayin. Kaga kuwa zaka iya, dan a baya sonka ya rufe mun idanu ta yadda bana ji bana gani. Ido da addini kaƙi fur a haɗa mu aure. Kaje ka auri sojar matarka siririya irin samburin matan da suke burgeka. Na roƙeka ka barni in auri namijin da yasan darajar ƙiba irin Gwadabe. Wanda zai dinga kammamani yana kuranta kyauna" Baki na tsuke nayi kicin_kicin. Daya isheni ma da magiya sai kawai na fashe mishi da kuka. Da ƙyar ya rarrasheni nayi shiru. "Shikenan Iyabo, zan sake baki lokaci. Ni gobe zan koma asubanci zanyi. Amman fa ki sani zan jiraki kije ki dawo sai muyi auren" Allah ya tsare ka gaishe mun da kowa da kowa. Banda matarka Yemisi, dan nayi imani batasan wajena ka tawo ba" Bai iya ce mun komai ba na yi tafiyata na barshi a wajen. Yaya Hamma kuma yana daga can gefe can gaba da inda su Daso suke tsaye. Dole ta gabansu zan wuce, hakan yasa saida na tsaya aka gaggaisa kana na Isa wajen Yaya Hamma Daso ta bini da idanu kawai. Zama nayi a gefen itacen da yake zaune, muka ƙurama juna idanu ƙur kamar zamu haɗiye junanmu. Idanunshi jawur harda kwantaccen hawaye marar yawa a cikin idanun nashi. Lumshe idanu yayi, yaja wani numfashi marar fassara a gareni, yai amfani da murya mai salon taushi da sanyi tarara wajen cewa. "Me yasaki kuka, kuma me Debisi yake nema a wajenki ne Jabu, na fahimci akwai babban sababin daya kawoshi rugarnan?" Ƙireni da idanu yayi. Nima ajjiyar zuchiyar na sauke. Na fayyace mishi ƙudurin Burodami Debisi a kaina. Na tsokata mishi ɗan labari akan cewar iyaye a baya sun haɗamu aure amman sai ya nuna baya ra'ayina. Amman na ɓoye mishi dalilin shi na ƙin nawa. Murmushi naga yayi har yanayin fuskarshi sai da ta sake. Gyara zama yayi yace. "To cika mun alƙawarina da kika ɗaukarmun akan kina dawowa zaki sanar dani dalilin zuwanki birni" Dariya na kwashe dashi, shima dariyar yake yi. Kwashe labari nayi na bashi. Da kuma dalilin da yasa zan tafi ɗin. Tashi ɗaya ya birkice har yana tsugunnawa akan guiwowinsa a gabana. Idanunshi suka cika fal da hawayen da suka kasa gangarowa. "Na roƙeki kar ki tafi Jabu ki barni. Shekara uku ban saki a idanuna ba, ai abune wanda ka iya kwantar dani. Ni zan siyar da saniyata in baki kudin a hannunki ki siya ma Dada gida, kiyi sana'arki da sauran kuɗin ki yi haquri ki janye wannan tafiyar dake shirin rabamu. In kuma ni kike so in mata duk abinda kike so a shirye nake. Yafendo uwatace, ina jin motsin sonta da tausayinta a raina. Jabu na roƙeƙi kar kiyi nisa damu, rayuka da yawane zasu jikkata" Mamaki ya kamani, to me Yaya Hamma yake nufi da wadannan kalami nashi? Ni ba yarinya bace na lura sarai tun zuwana yana ra'ayina. Amman ban tabbatarba sai jiya dana ga kishin Debisi ƙarara a idanunshi. Wannan kalamai nashi na yanzu sun ƙara tabbatarmun Yaya Hamma rainon sona yake yi. Kuma na fahimci Daso na tsantsar sonshi, Yafendo ma ta sani kuma tana fatan faruwar hakan. A duk sanda Yaya Hamma zai zo gida, sai Yafendona ta alaƙanta zuwan da Daso. Gashi matarshi ƙawarmu ce, mutuniyar kirki mai son jama'a. Kayi haƙuri ka tashi dan Allah yaya Hamma mu yi magana ta fahimta dan Allah " A tsugunne a gabana Daso ta iso ta sameshi. Numfashi ta ja tare da saurin yin turus, ganinta ne yasa ya tashi ya zauna. "Ki shiga gida Daso, ban gama magana da'ita ba. In muka gama zan rakota, ina buƙatarta tare dani" Fuu ta wuce har tana haɗawa da gudu. Tausayinta ya kamani, dan babu son da ya kai son maso wani ciwo, zafi ne dashi kamar zafin fitar rai daga gangar jiki. Mun fi awa ɗaya da rabi muna tababa tsakanina da yaya Hamma akan tafiyata. Bamu cimma matsaya ba Baffa ya fito ya korani ciki dan gaskiya dare yayi har ƙafa ta ɗauke magiya kawai Yaya Hamma yake yi tare da tambayata shanu nawa zai siyar ya bani kuɗin. Ko da na shiga bukkarmu a zaune ƙiƙam na samu Daso ta kurama aci bal_bal idanunta. Ledar gabanta ta turo gabana ina tsaye. "Ga saƙonki na wajen ɗan uwanki" Murya ba daɗi ta yi maganar. Ledar na ɗauka na zauna. A hankali na zazzaro kayan dake ciki. Kayan tea na gani, da macline da brosh, sai mayafai biyu, takalmi biyu da atampa ɗaya leshi ɗaya, sai zungureriyar wasiƙar da bani da niyyar karantawa. Biyu na raba kayannan cib na ba Daso, kayan tea ɗin kuma na ajjiye mana. "Ki riƙe abunki ni bana so" Wai Daso na yi miki laifine kike fushi dani. In akwai matsala ki sanar mun mana?" Na jefeta da tambayar ina ɗaga murya dan ta mugun ɓata mun raina ainun. "Hmmm" Shine iyakar abinda tace dani. Kayana na kwashe na mayar ko da na ɗane gado na kwanta Amman me? Sai bacci yace bani bashi. Tunanin Dada ya cakuɗe mun da tunanin furucin Yaya Hamma na ɗazu, da irin yanda duk ya kiɗime. Hasko mun da hoton Gwadabe da zuchiyata tayi sai hawaye ya soma tsiyayomun masu zafin gaske. Babala ta zalunci zukatanmu data ƙi amincewa mu rayu a tare. Nasan duk inda Gwadabe yake kuwa yana can zuchiyarshi a batse da kewata. A tsakanin ni da Daso babu wanda ya runta Washe gari sassafe ni da Hari muka gama duk aikin gida. Ina gama karyawa nai ma Yafendo sallamar ni zani gidan Baffa Musa. Acan na tarar mijin Dada yazo ɗaukarta, kuma abun haushin harta fito daga ɗaki ma suna tsakar gida. Da ƙyar na danne zuchiyata na bashi girmanshi albarkacin uwata da yake aure. Shi kuwa banza ya ba ajiyata, in kun tanka ya tanka. Har a kan fuskar Dada banga tayi farin cikin zuwan mijinta ba, fuskarta ma cike take da tsoro. Amman haka ya tusata a gaba suka tafi, ni ko da kuka na fice a gidan na dawo gida. Na tarar da su Yafendo sai dafa madara suke yi, taga na shigo da kuka kamar karamar yarinya dai. "Jabu lafiya kaddai Adda Daso mutuwa tayi?" Ganin yanda duk suka ruɗe suka yo kaina yasa na yi musu bayanin dalilin kukana. Yafendo da Hari ne su kaita rarrashina dai haka. Gaga_gaga haka rayuwa tai ta tafiya. Ko wacce rana kafin faɗuwarta sai hawayena ya zuba. Dada jikinta ya warware har ta soma fita tallar Nono. Sabida tsananin tausayinta yasa nake binta wajen sana'ar nonon nata. Sai tayi zamanta a gefen rumfa. Ni kuma ni zan zuba Nono in kai, in je in kwaso ƙworena. Munayin hakan ina jin daɗi itama tana jin daɗin hakan, dan karayar tata bawai ta warke sumul bane. Ƴan tsegumi suka sanarma da Mijin Dada ai ana ganinmu tare. Kwatsam muna kan siyar da Nono sai gashi ya zo dan ya zama ganau ba jiyau ba. Da ganinshi Dada jikinta ya soma mazari. Kwafa yayi kawai yaa bar tashar fu. Ranar dai haka muka ƙarashe kasuwarnan cikin taraddadi. Wannan shine silar da na dena bin Dada wajen sana'ar tata. Ta ɓangaren Hamma kuma shaƙuwar data shiga tsakaninmu shakuwace ta ban mamaki. Banda Dada da ƙannena,shi kaɗai nake gani ya yaye mun damuwata da kalamanshi masu sanya kuzari, gashi kullum sai naci tsire da lemun kwalba, Abunka da ƙauye tuni ƴan tsegumi suka tseguntama Hama ana ganin Hamma kullum da wata mace har dandali. Dan babu ranar da bama zuwa dandali, da Hama ta gane ai nice mijinta ke ƙwaƙwa, duk wannan far'a da haba_haba da take yi muni sai du ta dena. Har ta kai ta kawo ta dena kulani, ko na gaisheta ma da kyar take ka da baki ta amsa, harma abu ya zame musu rigima a tsakaninta da Boɗɗo. Daso kuwa tsakanina da'ita takun saƙane, taƙi ta yarda ba soyayya muke yi da Hamma ba. Tunda duk shakuwarnan bai taɓa cewa yana sona ko zai aureni ba. Ita kuma ma a lokacin har Baffa ya san da zaman Manga. Dan ance mishi zuwa kaka ya turo manya a gama komai. Ita kuma tayi tsalle ta dure kan cewar Allah ya kasheta bata son Manga. Baffa kuma yace ya bata kwana talatin ta fito da mijin aure in ba hakan ba ya aura mata Manga. Ni dai sai shirin tafiyata na sanya a gabana, nayi watsi da iskantakun Daso. Lokacin da labarin tafiyata ya shiga kunnen Dada bata ja ba, sai ma fatan samun nasara da tai mun. Baffa Musa ne yaso ya turje, amman su Dada suka haɗu suka tausheshi. Yaya Hamma dai ko hirar tafiyar tawa nayi mishi sai ya gimtse fuskarshi shi yasa ko zancan ma ni bana yi mishi, shima baya so, yayi juyin duniya in janye wannan tafiya. Ni kuma fur naƙi amincewa, har shanu biyu ya siyar da daddare sai ga kuɗi dumus nera na gugar nera har nera dubu ɗari cib Miƙo mun yayi nasa hannu na amsa sai naga kuɗine. Bayani yaimun akan siyar da shanunshi da yayi, duk dan kada in tafi. Ni kuma naƙi karɓa fur, na bashi hakuri tare da yi mishi bayanin na riga nasa Hajiya Salamatu ta kashe kudinta da ɓata lokaci. In nayi mata haka ban kyauta ba. Dole babu yanda ya iya haka ya mayar da kuɗin aljihun ƴar shararshi, tare da sauke kanshi ƙasa kawai. To ya akayi_ya akayi labarinnan ya je kunnen matar Yaya Hamma sai Allah. Nan ta da bori Boɗɗo na bani labarin irin rikicin da su ka yi ita da Yaya Hamma. Har sai da Yafendo ta shiga cikin lamarrin. Kuma jin abinda Yaya Hamma ya aikata yasa Yafendo ta fusata itama. Kun dai san fulani da maganar Shanu, dan tsabar ɓacin ran da Yafendo tayi ƙwace kuɗin tayi a hannun shi Yaya Hamman, tare da gargaɗin koma me zaiyi mun yayi mun ni ƴar uwarshi ce. Amman bata yadda ya sake taɓa shanu ba, waɗannan shanu gadon_gadone da suke fatan ƴaƴansu Hamman da jikokinsu, da haularsu masu zuwa suita gadansu. . Ana saura sati guda in tafi, sai Yaya Hamma ya soma rashin lafiya. Abu kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Tun yana zuwa kiwo har dai ya dena. To dake a ɗakin Yafendo yake jinyar tashi, ana saura kwana biyu in tafi sai na je dubashi. Ina shiga sai Hama ta bar duk abinda take yi ta dawo ɗakin Yafendo ta zauna. Harma tana shafan sumarshi a gabana dan inji haushi, shi kuma kunyata tasa ya ture hsnnunta. Ai ko abun ya mugun sokar zuchiyata ta yadda ni kaina sai da nayi mamakin yanda naji sautin kishin mutumin da bai buɗe baki ya furta mun kalamin so ba. Sai dai iya so da kulawa a aikace yana nuna mun. A furucine bai furta ba, kuma na fahimci nauyi abun yake yi mishi. Kunya da kawaici irin na fulanine ya hanashi furta mun yana sona. Shigowar Yafendo da fura a hannunta ne yasa Hama tashi ta dawo ƙasa ta zauna. "Jabu ga fura ki sha" Ta miƙo mun. Hannu biyu nasa na amsa nace. Use Yafendo. "Hama kin baro aikin ki kin dawo kin zauna? Maza tashi ki koma kan aikin ki, kinsan zaki je tallan nono fa" Har cikin ranta bata jin daɗin wannan katsalandan da Yafendo tayi mata ba. Amman ni kuma kamar in goya yafendo haka naji" Tare suka fice ɗaki ya rage daga ni sai Yaya Hamma. Shi kuma fishi sosai yake yi dani duk fa akan tafiyar tawa ne. Ni sai tafiyar ta fitar mun akai, kuma nayi mishi rantsuwar da ace da kuɗina akayi mun komai da tuni na fasa. Amman yanzu in nace na fasa hajiya Salamatu ba ƙaramin bacin rai zata nuna ba, kuma ƙila ita kanta uwani in ja mata. Yaya Hamma ya jikin naka?" "Da mutuwa ma zanyi kila hankalinki sai yafi kwanciya ko?" Sai naji faɗuwar gaba har idanuna suka kawo ruwa. Cikin rawar murya nace. Ko kusa bazan ji daɗi ba. Kayi haƙuri tafiyar da zanyi ta dole ce, kuma bazan shige shekaru uku ba zan dawo. Kuma ina fatan in dawo in sameka a cikin aminci. Ɗan murmushin gefen baki kawai yayi mun. "To ki shirya tare zamu tafi kanon. Bazan dawo ba har sai jirginku ya tashi. Idanu na zaro nace. Ka rufa mun asiri kar kasa matarka ta bindigeni. Kai da baka da lafiya kuma sai in ɗaura maka wahala? Wallahi ka barshi. Hararata yayi mai cike da tsantsar so. "Ai ratayayyen hakkine a kaina inga tafiyarki." Shiru nayi zuchiyata na doka mun tambura. To Allah ya baka lafiyar Yaya Hamma. Ni zan zo in wuce" Sallama nayi mishi na fito da furata a hannuna a ɗakin Boɗɗo na shanye furata. Washe gari Dada ta kawo mana ziyara da su Cubu dan muyi sallama. Tayi mun nasiha mai ratsa zuchiya sosai. Nayi kuka kamar raina zai fita. A daren na kasa baccin kirki. Ina kwance Daso ta shigo ta tsaya a kaina. "Sai ki tashi Yaya Hamma na kiranki. Jabu wallahi kiji tsoron Allah kinzo kin samu mutum da ƴar matarshi suna soyayyarsu gwanin sha'awa. Amman kinzo kin raba wannan soyayyar da shaƙuwa, kin hana Yaya Hamma ya samu lokacin kan shi balle ita Matarshi ta samu lokacin shi itama" Tashi tsaye nayi ina jujjuya maganganun da Daso ta fesomun. Kai kawai na girgiza tare da cin alwashin sai na jero mata waɗanda suka fi wanda ta faɗa mun zafi. Ficewa nayi na barta da ƙunan zuchiya. A zaune na sameshi yana zane a ƙasa da tsinke. Zama nayi a gefe nace. Barka da zuwa Yaya Hamma. Yaya jikin naka amman?" "Jiki da sauƙi Jabu. Ya shirin tafiya? Nasan dai an gama komai ba tun yau ba. Ke naga zumuɗin tafiya ki barni kike yi" Sai naji duk jikina ya mutu. Shine yake ganin kamar ina zumuɗin in tafi in barshi. Amman har cikin jikina inajin zafin kewarshi tun yanzu, bansan kuma ya abun zai zama in na tafi ba. A ranar dai hirar batai armashi ba jikkunanmu a mace mu kai sallama. Harna taka zan shiga gida ya kira sunana. "Jabu" Cak na tsaya. A hankali na juyo muka zuba ma juna idanu na mintunan da bazan iya faɗar adadinsu ba. Ya kasa ce mun uffan. Fitowar Jatau ce ta katse komai. Bai samu damar faɗa mun abinda yasa ya kirayi sunana ba, Jatau ya tareshi da zantuttuka. Cikin na shige na barsu nan. Ina shiga na harari Daso nace. Gobe zan bar garin. Kinga hakan zai baki damar cusa kan ki a wajen Hamma. Kinga in da rabo sai in dawo in sameki kina goyon ɗanku na biyu ke da shi." Ina faɗin haka ta kalleni tace.."haka kika ce mun Jabu?" Ƙwarai kuwa haka nace. In kin isa ki maye gurbina a zuchiyarshi in zaki iya Ni kin ganni nan tafiyata tafi komai mahimmanci a wajena" Kwafa tayi tace dani. "Zan baki mamaki Jabu, zaki san nima macace wacce Allah ya horema duk abun alfahari kinsan dai na fiki kyau nesa ba kusa ba, in banda ma namiji da gane_gane ko me ya gani a jikinki oho" Ni ban ma sake bi ta kanta ba. Itako sai mita take yi da fillanci. Ina kwance shiru duk kewan yarana ya kamani, dama Baban yaran. Can kuma sai Hamma ya fado mun, da kuma alwashin da Daso taci mun. Da irin wannan tunani bacci yayi awon gaba dani. Asubar fari na yi wanka tsab. Ana fitowa masallaci na suri kayana a jakar leda na fito. Na yi sallama da kowa da kowa. Ana cikin haka Yaya Hamma ma ya shigo. Muna fitowa Boɗɗo da mijinta na isowa suma. Sai da suka rakamu fa har Girai kana suka dawo mu kuma muka shiga cikin gari, Yaya Hamma ya samu a motar Kano. Sassafe motarmu ta hau kwalta. Sai da tafiya tayi nisa Yaya Hamma yace. "Inaso ki mun wani alƙawari Jabu. Nasan kina da riƙon alƙawari na san hakan silar shaƙuwarmu. To ki mun alƙawarin da kika tabbatar zaki cika mun shi. Kar ki yaudareni in yayi miki tsauri ki ce mun ba zaki iyaba" A sanyaye nace dashi. Faɗi alkawarinka a shirye nake da in cika shi. Matsayinka ya wuce hasashenka" Daɗi yaji sosai. "Ki mun alƙawarin ba zaki wuce shekaru ukunnan da kika ɗebarma kanki ba. sannan ki mun alkawarin ba zaki kula samari ba dan Allah. Sannan ki mun alƙawarin ba zaki dawo kiji ke kinfi ƙarfin zama tare damu ba. Bi ma'ana kar ki sake halayyarki, sannan ki mun alƙawarin riƙe mutuncinki" Shiru nayi mishi ina murmushi kaina na ƙasa. "Au ke dariya ma na baki ko? Kin kyauta ai" Ɗago kaina nayi na kalleshi. Yaya Hamma na karɓi duk alƙawarurrukanka. Allah yai riƙo da hannayena in cika maka alkawarurrukanka. Amman ina da taambaya..." "A'a Jabu ".. yayi saurin dakatar dani ta hanyar ɗaga hannayenshi. Ba shiri na yi shiru da bakina. "Ni dai tunda kin ɗaukii dakon alkawarina ai Shikenan. Ni kuma zan yi zaman jiran dawowarki, tare da miki fatan samun nasara kuma" Daga haka kuma mu ka ɓige da hirarraki, ya dinga bani labarai dangane da al'adun Fulani. Ni kuma dama na kasance ma'abociyar son tarihi ce da duk abinda ya shafi gargajiya ta ko wanne ƙabila. Allah cikin ikonshi da amincewarshi muka isa garin Kano. Kai tsaye gidan Uwani muka ya da zango. A gidanta muka ci abinci. Yaya Hamma ya fita zuwa masallaci dan rama sallolinshi, nima na rama nawa sallolin. "Baki ga yanda kuka dace ba wallahi. Ashe kyakkyawane Yaya Hamman naki. Kuma na lura gaskiya yana tsantsar sonki. Munafuka kema fa kin soma sonshi. Ni dai amman bana bayan wannan soyayyar ruga ba wajen zamanki bane" Dariya mu ka yi dukka. Hakane Uwani wallahi na tsunduma cikin sonshi. Shi kuwa dama ba'a magana dan shi ya koya mun yanda zan so shi. Sai dai fa akwai kura Uwani" Sai da ta gama dariyarta tas kana tace mun. "Ƙurar me kuma Iyabo, akwai wata matsalar ne?" Nace da'ita. E to akwai matsala ta ɓangaren matarshi, da ɓangaren yarinyar ƙanwar Dadanmu Daso wacce nake gidansu a zaune. Matsalolin du manya ne daka iya dakile soyayyarmu. Matarshi tunda aka kai mata gulmar ana ganin mijinta a wajena, sai ta tayar da ƙayar baya, kullum cikin fitina dashi take. Ke har shanunshi daya siyar ya bani kuɗin ban karɓaba sai da su kai rikicin da har mahaifiyarshi ce ta shiga. Ƙanwata tana Aure a gidan Uwani tana auren ƙanin shi hamma ɗin. Sai suka tsiri zaman doya da manja. Ita kuma Daso ko tsaiwa da zaurawa bata son yi kwata kwata duk sabida da shi. Akwaifa wani abokin mijinta mai rasuwa da yake tsantsar sonta. Yarinyarnan fur ta dire wai bata sonshi. Ni kumaa a jiya ta caccakamun magana akan wai Hamma na zaman soyayya da matarshi ni nazo shiga tsakani na hana aci soyayyarnan yadda ya dace. To kinsan mu mata, saina caccaka mata nawa maganganun nace ta aurshi in dawo in samu tana goyon ɗansu na biyu. Ita ma cikin fishi sai tace zan gani. To jiya da ƙyar nayi bacci Uwani " Dariya muka dinga yi ni da Uwani. "Ni dai shawarar da zan baki wallahi ki raba kanki da wani auren ruga, kiyi fatali da wani Hamma. Kinga ƙasar zamu bari Iyabo soyayya ba taki bace. Shigowar Yaya Hamma da Hafizu ne ya dakatar da tattaunawar tamu. Sun zauna babu daɗewa nace. Uwani Hafizu mu kam zamu tafi gida. Sai gobe kuma in Allah ya nuna mana." Tare su kai mana rakiya izuwa titi har sai da Bus ɗinmu ta tashi sannan suka juyo. Kwatsam su Iyaa suna tsakar gida suna wannan hira tasu mai kamar faɗa muka shigo. "Ah Ah ah ah Iyabo. Ikabo ( sannu da zuwa)" Nan ta miƙe ta soma rawa harda guntuwar waƙarta su Iyaa Beji na mata dariya. Dukkansu saida na bisu ɗaya bayan ɗaya na dinga zubewa a gabansu ina kwasar gaisuwa bisa ga al'adarmu. Yaya Hamma dai duk abinda yaga nayi shi yake maimaitawa. "Lekan, Lekan woo ah" Lekan ya amsa da karfi sai gashi harda gudu. "Ahh Antimi Iyabo Ikabo o ti dara osale ( Anti Iyabo Sannu da zuwa Ina wuni?)" Owo bawo ni o se n se? ( Yaya kake Lekan)? Nima na tambayeshi da yarenmu. Hannu ya miƙa suka gaisa da Yaya Hamma kana yace mun. "Owo mo dara Antimi ( Ina lafiya Anti) "Mu u lo si yara re ( Kai shi ɗakun ku) Cewar Iyaa. Ni kuma ta jaye hannuna muka shige ciki. "Ashe dai zaki zo Iyabo? Nayi kewarki sosai. Sai inta mafarkin ki. Har sai da Debisi yaje ya dawo ya tabbatar mun kina lafiya sannan na samu nutsuwa. Sai kika ga Debisi ko?" Murmushi nayi mata nace. Sai gashi Iyaa babu zato" Dariya tayi kawai kana tace. "Duk abinda babba ya hango yaro ko ya hau bishiyar rimi ba zai hango ba. Dama dan ya samu nutsuwa ne yasa na ce ya aureki dan zaki fi ganin darajarshi da kimarshi sama da ko wacce mace. Amman sai ya nuna shi baya so. To wacce yake so din gasu can kullum cikin faɗa, ko jiya uwar haka suna gidannan anata shari'ar da ni na gaji da'ita. Yanzu dan Allah da ke ya aura hankalinshi ba kwance ba?" Kasa amsata nayi, dan da kunya Debisi dai ita ta tsugunna ta haifeshi. "Shi wannan ɗin da ya rakoki ko shine oko omo obirin ɗin nawa? (Sirikina). Kai na sauke ƙasa nace. A'a yaron Ƙanwar Dada ne. Dama zan tafi saudiyya aikataune shine ya biyoni in mun tashi sai ya koma shi kuma" "Ah Ah orira ( abun mamaki) Saudiyya fa kika ce?" Sai ta miƙe ta shiga rawa tana jero mun waƙoƙin sanya albarka. Har sai da ta tara mun matan gidan. Nan take kowa yaji abinda ke faruwa. Nan gidan ya kacame da waƙoƙi da murna. Bayan sun tafi ne Iyaa ta bani Amala tace. "Ki kaima Ɗan uwanki amala yaci abincin yarbawa" mayafina nasa na ɗauki kwanon na fice zuwa ɗakin lekan. Da sallama na shiga na samu yana kallon wani film na yarbawa. Shi kaɗaine a ɗakin sai lemun kwalba na limca dake gabanshi. *Ƴar uwa ina fatan baki mance da kayan ƙamshin Mrs Bukhari gidan ƙamshi ba ko? Ƴar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ƙamshi. Matso kusa ƴar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ƙamshi ya riƙe miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake saƙawa a tsakankanin kaya. Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ƙamshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata. Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haɗe da turaren fesawa a gashi. Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ƙara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ƙamshin kifi ɗanye. Inada humrori kala_kala. Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ƙamshi. Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ƙamshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ƴar mutan Maiduguri kin samu ƙamshi. ( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai ɗauke da abubuwa huɗu manya kuma a kan kuɗi ƙalilan karki bari garaɓasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)* NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE.... LITTAFI NA BIYU 3 A hankali na isa na zauna a gefenshi. Idanu kawai ya zuba mun sai naga yana kaɗa kai.. Kwanon abincin na tura mishi gabanshi. Ga Amala abincin bugun gaban yarbawa da fatan kana iya ci" Dariya yayi mun yace. "Tun kafin ki zo duniya nake cin Amala. Ai nayi zaman oghomosho, sarkin garin Oghomoshon ma bafulatanine. Kinsan tun shekaru aru aru yarbawa suke a matsayin bayin Fulani. Hakanne yasa auratayya tayi ƙarfi a tsakanin Yarbawa da Fulani. Sai kiga bafulatani sak amman sai kiji bai iya ko fillancin ba sai yarbancin. Haka sai kiga beyerabiya na zagargaza fullanci. Ki duba Dada yanda naga da yarbanci zalla take magana dake." Ajjiyar zuchiya na sauke nayi dariya. Shima dariyar yayi ya soma kantara lomar Amala miyar ewedu sai dalali take yi a hannunshi. Sai da ya cika bakinshi da ( phomo) ganda kana yace. "Ni ko kibar matan yarbawa na birgeni, kuma Allah ya zuba musu sura masha Allah ." Dariya nayi sosai nace. Ku da kuke da farare kuma siraran mata masu gashi" Dariyar shima yake yi mun. "Jabu kenan. Ai cikakkiyar mace ƴar duma_duma daban take da siririya. Shi kyau a sura yake ba'a fuska ba ai. Bance sirara basu da kyau ba. Kuma bance yarbawa sun fi filani kyau bane. So nake ki fahimta, wani namijin mai sha'awar haɗa shinkafa da doya ne. Wani kuma taliya kaɗai ta wadatar dashi" Cikin karantar yanayinshi nace dashi. To kai a wacce matsayar kake ne?" "Koma a wacce nake zaki sani ne" Cikin raha dai mu kaita hirarmu har ya kammala cin abincin nashi. Kana nayi mishi sallama na tafi. Sai zuwa washe gari na haɗu da su Burodami kokodeen da su Burodami Debisi. Kuma na zagaya gidajen nasu naga yaransu, na gaisa da matansu. Yemisi dai babu yabo ba fallasa, dama ya lafiyar kura ballantana tayi hauka. Haka dai akaita mana shirin tafiya, dan har munje anyi mana gwaje_gwaje iri da kala a asibiti. Ana washe gari zamu tafi ko bacci na kasa yi dan dadi, da kuma wata fargaba data lulluɓeni. Burodami Debisi, da Yaya Hamma, da Hafizu sune abokan rakiyar tamu har zuwa filin jirgi, ko ince ɗakin jira. Gefe guda muka keɓe da Yaya Hamma da jikinshi naga har rawa yake yi, idanuna a cike da ruwan hawaye. Naso Yaya Hamma ya furta mun kalmar so kafin in tafi ya jaddadamun matsayina a zuchiyarshi. Amman kunya da ƙauyanci ya danneshi. Haka dole mu kai sallama ba tare da naji inda soyayyarmu ta kwana ba. Ko da muka shiga cikin Bus ɗin da zata kaimu gaban jirgi ai sai na sake fashewa da kuka, ina tunano fuskar Yaya Hamma, da yanda yake ta aukin jaddadamun alƙawarinmu. Burodami Debisi kuwa kamar ya shaƙo Yaya Hamma ya rufeshi da duka haka yake ji. Gurin dake ɗaure a shintsiyar hannunshi daya bani na sake damƙewa a hannuna. Yau ni Iyabo gani a cikin jirgin sama zai tashi damu zuwa ƙasa mai tsarki. . Hukunci sai mai tsaga idanu. Allah sarkin girma in ji kishiyar mai duwawu. Maraɗi Gwadabe:. Auwala bai dire Sabitu a ko ina ba sai a gaban malam, ga almjirai cike da wajen. Tun kafin Malam yayi magana. Baba Asshi ta fito babu ko mayafi a jikinta. Kallon da taga gardawan Malam Magaji na yi mata ne yasa ta koma daga zaure. "Auwala wannan wanne irin riƙo kayi mishi kamar ka kamo barawo" Malam ya girgiza kanshi yana bin ƙofar zauren da kallon baƙin ciki. Baba Fhatsima ce ta fito saye da katon mayafinta ta jaye Hadiza tare da cewa. "Koma me ya faru a barshi a tattauna a cikin gida. Auwala cikashi, kai kuma Sabitu jeka abinka. Allah yayi muku albarka baki ɗaya. Hadiza ta jawo suka shigo zauren Baba Asshi ta harareta sama da ƙasa tace. "Ni nawa yaran sai ki tsine musu ai, tunda naki kika sama albarka. Ni na ji jaraba fa, kun bi kun sani a gaba Fhatsima kin hana mun jin daɗin aure" Baba Fhatsima Taso tsaiwa ko wacce zata hanata bacci ta feso mata. Auwala sai ya kama hannunta suka shige. Su kuma su Gwadabe suka wuce barayinsu dan watsa ruwa su ji daɗin jukkunan nasu. Gwadabe yana wankannan yana tunanin me yasa gida in da mace sama da ɗaya ake yawan samun rabewar kai ne. Ta ina kuma matsalar tafi rinjaye tsakanin matan, ko uba da yake zama majingina a wajen mata da yaran gida.? Da wannan tunanin ya fito. Fitowarshi ke da wuya Ine tazo ta yi kiransu gabaki ɗaya harda Gwadabe izuwa turakar Malam. A babban falonshi duk suka gurfana Malam ya soma magana da cewa. "A wannan karon duk macen data nuna zata kawo mun rabewar kan ƴaƴa ni zan iya sallamarta ta tafi gidansu. Allah yana gani daidayya ina bakin ƙoƙarina dan ganin nayi adalci a tsakanin matana harma da su yaran nawa. Ke Fhatsima kece Babba a gidannan na faɗa ba tun yanzu ba zan haɗe kan yarana da matansu dukka a gida ɗaya dan su rayu tare yaransu su cuɗu da juna ta yadda zasu shaƙu da junansu. Wannan magana tamkar a rubuce take ba fashi. Duk da Asshi ta nuna ita bata bukatar a haɗe yaranta dana Fhatsima. Harma Jamilu ya goyi bayanta a kan hakan. Rikicin Sabitu da Hadiza ne yasa na dawo da wannan maganar baya. Nasan ko wacce nayi mata bayani ita kaɗai Amarya malam uwar kissa ta dubeshi da taushin murya tace. "Allah shi gafarta malam ni nawa yaran da suka kasance ƙananu ya za'ayi dasu to?" Dariya malam yayi cikin so yace. "Amarya harda su Rabi'u za'ayi wannan ginin. Su kuma mata _matan da zasu yi aure ko wacce zan bata kadara a matsayin kyauta, kanana marasa aure kuma sai in ajjiye musu zuwa lokacin da Allah zai ƙadarta su yi aure. In kuma ta Allah ta kasance a kaina sai a danƙa musu baya cikin gado na basu halak malak, hatta ginin da Shi Tasi'u zai musu baya cikin gado na mallakawa kowa halak malak harda Gwadabe dan gudun kar in kwanta dama tashin tashina ta tashi. Dan kuna ganinane kuke samun damar faɗace_faɗacen nan da kuke yi. Wallahi duk ranar da za'a wayi gari bana doron ƙasa zaku yi dana sani, za kuma kusan mahimmancina. Zaku iya tafiya" A lokacin dai jikkunansu duk ya mutu, amman kowacce tana jaye ƴaƴanta suka shige ƙurya sai labari yasha banban. Wannan kyauta da malam ya furta bata cikin gado itace ta tayar da ƙayar baya, baƙin ciki da hassada ya shigo, musamman ga wadanda basu da damar cin tudu biyu. Haka bikin yaran gidan yaci gaba da matsowa, sai shirye_shirye aketa ta faman yi kowa ta ciki na cikinta. Yaya Tasi'u da matarshi Anty Badi'at ba zama, dan ita ta shiga cikin nijer ta siyo kayan gadajen Amare da kayan kitchen ita da Amaryar Malam. Kwana bakwai da Baba Magaji ya ba Gwadabe ta cika, Baba Magaji baice komai ba, shima Gwadabe yaƙi cewa komai, zuchiyarshi kullum cikin taraddadi take kawai, har aka tsunduma sha'anin biki dai Baba Magaji na kallon Gwadabe ya zuba mishi idanu. To al'adar auren Maradi ya banbanta da al'adar aure a Najeriya ƙasar hausa. Su yanda suke bikinsu shine. *KAN GORO* Shi yanda ake yinshi shine. Iyayen Ango zasu tawo da goronsu a jarka za'a daddaleshi, yana danganta da yanayin karfin miji. Zasu tawo da balis ( Akwati) wasu suna zuba kaya a ciki, wasu kuma basa zubawa, zasu tawo da kuɗin sadaki, da hidimar girke_girke rigi_rigi. Iyayen Amarya maza su kuma zasu zauna a manyan taburmai domin tarbar iyayen ango da wannan kaya. Iyaye mata a gida kuma zasu yi girki na alfarma a fito dashi. Anan za'a tsayar da lokacin Aure da bai haura wata guda ba, wasu ma sati guda ya danganta. To su dangin Ango zasu tafi da wannan gara ta dafaffen abinci tare da tsayayyen lokacin Aure. *LIFARAN* shi kuma lifaran ( Anko) ake nufi. Daga kawo wannan kayan aure da kuɗi. Dangin Ango, da dangin Amarya sai su fidda Ankon biki. *LALLE* Amarya zasu zauna zaman lalle na kwana biyu ita da ƙawayenta. *KUƊIN SIGA* Shi kuma kuɗin siga kuɗine da dangin Amarya suke hidima dashi ma dangin ango. Akwai kuɗi uwa ko kuma ai mata kaya, da su saitin bahuna, da turmin zani na goyo. Shi wannan setin bahunan da turmin zani ana bayarwane a matsayin an mayarma da uwa zanin goyo da bahunan wankan Ango lokacin da yake jariri, da sontolon tsaba duk na uwar miji. Sai buhunhuna hatsi na gara bana wasa ba. Hatta facala in amarya na da shi akwai kudinta, kudin abokan ango na zirga_zirgar biki, sai buta da Dadduma, da jikka biyu na kudi na uban miji. Baki ƴan nesa kuma da suka tawo biki, ana zuba tsaba a roba da turamen zannuwa a basu. Su kuma sai su ba da jikka goma na uwar Amarya a matsayin tukuicin wannan hidima ƊAURIN AURE. Su kuma da safe akeyin ɗauri in dai na budurwane. Sannan ana fitarma da maza ƴan ɗaurin aure abinci waje aci asha a goge wuya. *WATSI* Wannan ɓangaren gidan ango ke yi. Bayan isha ko bayan magriba za'a shinfiɗa tabarma a zaunar da ango a tsakiya. Ai ta mishi watsin cingom da kudi shima ya danganta da ƙarfin dangin ango, amman a wannan watsin ango na samun kudi ainun. ƊAUKO AMARYA Bayan an gama watsi kuma dangin Ango zasu je su ɗauko Amarya a kaita ɗakin mijinta. Iyaye suna yin hidimar kayan ɗaki sosai, gado biyu suke yi, banda kafet_kafet da manyan daddumai. *YININ BIKI* Shima bikine rigi_rigi ake yinshi, sannan a yinin bikinnan suke sa anko dangin ango dana Amarya. Ayi yinin biki a watse shikenan biki kuma ya ƙare. Daga cikin wannan sha'ani na biki babu wanda aka raga. A zahirin gaskiya an kashe kuɗaɗe sosai, duk wata hidima da akayi Tasi'u da matarshi ce suka gudanar da duk wani kashe kuɗi. Gwadabe kuma a lokacin sha'anin bikinne ya karema ragowar ƴan matan gidan kallo tsab. A tsahirance sunfi Hadiza kyau ta fuskokinsu, sai dai ita kuma Hadiza ta fisu diri da kiba, dan shi kuma baya sha'awar mata sirara sam. Da wannan dalili nashi ne ya ƙudurce a ranshi da zaran an watse biiki zai tunkari Baba Magaji da batun Amincewarshi ga Hadiza. Ga Tamu ko da yaushe su kai waya yakan yi mishi tuni da batun ƙanwarshi da take zaman jiran Gwadaben. Harma sun yi waya sau biyu haka. Yanda ya ɗan taɓa hira da'ita sai yaji babu dai wata matsala a tattare da'ita ko na rashin tarbiyya, ko na fitsara irin ta wasu matan. Ƙarshen wayarshi da Tamu a cikin hidimar bikinnan yake cewa da Gwadabe. "Gwadabe duk ɗan abinda ka rarumo na kudin moya kazo ayi aurennan kowa ya huta. Bara'u yace ya ɗauke maka sadaki. Ni kuma zanyi mata akwati da kaina. Aure kawai zaka zo a ɗaura, sabida manema sun soma damunta, duk da dai bata ƙarashe karatun ba amman ƙiris ya rage' Jin wannan batu ne yasa Gwadabe kiran Bara'u yai mishi bayanin halin da yake ciki akan ɗiya da Baba Magaji ya bashi harma da kyautar wajen zama. Bara'u shi kuma ya tafi kafa da ƙafa har Habuja su kai magana da Tamu. Ya nuna ai wannan ba komai bane, Gwadabe mijin mace huɗu ne bama biyu ba. A take suka kirashi suka tsaida magana kan da zaran yarinyar ta gama karatunta za'ayi auren. Ƴan biyu dake hannun Tamu sai wayau suke yi, suna karatunsu hankali kwance. Ayashe tana riƙe dasu da amana ta game yaran da nata ta maishesu tamkar yaran data tsugunna ta haifa. Haka ma Toye yana zuwa makarantar boko data allo, suna zuwa gona yin noma. Dan Bara'u ya siya musu ƴar ƙaramar gona da yaron wajenshi, harma bana sun noma gyaɗa na kwano uku, da taimakon Sakina dake rakasu gona tana kuyi wannan ku bar wancan Amare sun tare a gidajen mazajensu lafiya, hankalin iyaye ya dawo jikinsu kuma kowa ya ci gaba da sha'anin gabanshi. Wata ranar talata da daddare bayan su Gwadabe sun gama karatun dare sai ya nemi ganawa da Baba Magaji kan batun Hadiza. Dan yaga tun bayan da aka yi bikin gidan. Sai zawarawa suka shiga zurubtu akanta, suka shiga hidimar kashe mata kudi. Dan samarin nijar jaruman gaske ne akan matansu. "Baba Magaji dama akan maganarmu ne da kai. Shine nace na zaɓi Hadiza kamar yadda kaima ka zaɓa mun tun farko. Sai dai akwai ƙanwar abokina Tamu da shi Tamun ya bani tun kafin in tawo nan ɗin. Shine nake tunanin in ka amince sai a haɗa tare ayi bikin lokaci guda. Tunda ita yarinyar kafin lokacin da aka kintata na bikin zata kammala karatun da take yi." Ƙur Baba Magaji yayi yana kallonshi ya jima baice komai ba yanata jujjuya maganar Gwadabe a kanshi. Yana kuma hango irin gagarumar matsalar da ka iya bullowa. Wanda ada ita ya guda, sai gashi ta kuma biyoshi. Bayan dogon nazari da Baba Magaji yayi sai yace. "To Gwadabe naji duk bayaninka. Kuma na gode da nuna sonka da auren Hadiza. Wani hanzari ba gudu ba Gwadabe. Hadiza macace mai ɗan banzan kishi ainun. Kaga kishi? Shi ya hallaka igiyoyin aurenta na baya. Abinda yasa na soka da Hadiza, yarinyace mai biyayya batta da kishi dai. Nayi tunanin kuma ba lallai ka rakito wani auren nan kusa ba, duba da sana'ar taka ma da kake yi har yanzu baka da ido akanta. Kila ko da zaka yi auren sai nan gaba, kila a lokacin Hadiza ta zama babbar mace ka samu sassauci. Kaga mahaifiyarta ko? A lokacin dana auro Asshi sai da muka shafe tsawon shekaru biyu da rabi bata haɗa shinfiɗa dani ba. Kai ƙafarta bata sake taka turakata ba, har sai da santa yaimun lahanin da ya kusan rabani da rayuwata kafin. Gwadabe ina son Fhatsima fiye da yadda kake tunani, kuma ina matukar girmama duk lamarinta. Bata taɓa yin hayaniya ko musu dani ba. Shawarar da zan baka shine. Kaje ka auri ƙanwar Tamu ɗin, ita kuma Hadiza Allah ya fito mata da wani mijin. Gudun kar zumunci ya taɓu dukkanku ƴaƴanane. Tashi kaje Allah yai maka albarka". Gwadabe yaso Baba Magaji ya bashi dama yace ko da wani abune. Amman sai ya ki bashi wannan damar haka dole ya tashi ya tafi. Kuma tsakani da Allah Hadiza ta kwanta mishi fiye da yanda ƙanwar Tamu ta kwanta mishi. Dukkansu a cikinsu baiga na ajjiyewa ba, abu suka haɗe mishi goma da ashirin, ga tunanin Iyabo wanda yake ɗamfare a zuchiyarshi babu dare bare rana. Da Hadiza yaci karo a zaure zata fita taci kwalliya da bakar lafaya ta zubo gashinta gaba. Murmushi ta sakar mishi da ganinshi. Shima yai mata murmushin tare da cewa. "Sai ina da wannan kwalliyar kamar zaki gasar sarauniyar kyau?" Dariya kalaminshi suka bata, sai da ta dara kana tace. "Sallama akeyi dani a waje Yaya. Bansan ma ko waye ba" Sai yaji nan nake kishi ya lulluɓeshi dan ai Gwadabe gwanine na ƴan kishi mun sani tun a baya. Ƙin magana yayi da yaga tana shirin wuceshi ne yace. "Ke daga an aiko ana kiranki sai ki fito harda caɓa kwalliya haka? To maza ki koma Baba batai miki bayanin suna son haɗamu aure bane, ko ni dinne bakya so talaka?" A zabure ta ɗago ta kalleshi cikin maɗaukakin mamaki. Shi kuma yai tsai yana karantarta. A madadin yaga damuwa sai yaga akasin hakan. Dan bata san sanda ta kwashe da dariya ba, ta juya ta shige gida da sauri halamar dai itama fa tana ra'ayinshi yayi mata. Kanshi ya dafe tare da jin haushin kanshi kan furta wannan kalma mai nauyi. Tsoronshi Allah, tsoronshi kar sanadiyyar aurensu zumunci ya taɓu. Dan ƙasan zuchiyarshi gurbin son iyabo ne, tsakiyar zuchiyarshi kuma na ƴaƴanta ne. Ko wacce irin macece zata rayu dashi sai dai ta rayu dashi a saman zuchiyarshi. Yana tsoron rashin adalci, yana tsoron fitinar mata biyu da rabe_raben kan ƴaƴa irin na gidan Baba Magaji. To wacece ta cancanta Gwadabe ya aura a cikin mata biyunnan? Wani shashe na zuchiyarshi yace. "Ka ba ko wacce daga ciki lokaci ta fayyace maka irin sonta, a ciki sai ka zabi guda, guda kuma ka bata haƙuri. Cikin rashin tunanin abinda hakan ka iya haifarma ɗaya daga cikin matar da za'a ba hakuri Gwadabe yai na'am da shawarar zuchiyarshi ba tare da yayi hangen nesa ba. Wannan shi ake kira nama ya dahu romo ɗanye. Nan Gwadabe ya raba lokacin shi ta hanyar rabashi a tsakanin Hadiza, da Shafa, Hadiza suna keɓewa suyi zance, yayin da Shafa kuma yake kiran wayarta su sha hira. Yana auna kalaman ko wacce a zuchiyarshi, yana nazari dan gano wacce tafi sonshi da nuna tausayinshi. Tun Baba Magaji bai san Gwadabe na zance da Hadiza ba har mata suka tsegunta mishi. Kuma Baba Fhatsima, da yaya Tasi'u, harma da su Auwala sun aminta da wannan haɗin kuma sun yi farin ciki sosai. Baba Magaji ranar yaso su tattauna da Baba Fhatsima akan batun Hadizan da Gwadabe, kasancewar ranar ita ke da miji. "Fhatsima naga kamar Hadiza ta amince da soyayyar Gwadabe ko?" Ya jefo mata tambayar yana daga kwance, ita kuma tana kasa a zaune tana dama mishi furar da duk daren duniya sai ya sha kafin ya kwanta. " Kwarai ko. Nima kuma na daɗa ƙarfafarta naga Gwadabe yana da hankali." Kai Baba Magaji ya gyaɗa yace. "Hmm Hadiza kenan. To abinda ta guda a gidan uban yaranta shine ya sake biyota. Kishiya ba? Dan abokin Gwadabe Tamu ya riga ni ba Gwadabe ƙaunarshi, kuma ya riga ya karɓa tun kafin yazoshi. Ni da naso dakatar dashi neman Hadiza dan harna sanar dashi dalilin mutuwar aurenta na baya. Amman bamu san me Allah yake son nunawa ba akan hakan, ƙila wata ayar zai saukarma mata masu kaso aurensu sabida kishiya. Allah ya daidaita tsakaninsu" Shiru Baba Fhatsima tayi kawai. Furar da take damawa ta dakatar da damata. Lokaci guda ta jagule. Hakan yai sababin sawa Baba Magaji ya mike zaune ya sakko ƙasa daf da'ita. Yayi ƙasa da muryarshi yace. "Fhatsima kiyi haƙuri a bisa kalamina. Allah ya sani ba dake nake yi ba, da ita Hadiza nake yi. Amman kiyi haƙuri" "Hmm Malam kenan. Ashe nuna kishi ga abinda kake so matsalane a wajen maza mu bamu sani ba? Tunda nake kishina a gidannan tsawon shekaru fin talatin ka taɓa kamani ina shirka, ko na taɓa tayar maka da hankali ne? Ai ko Hadiza batai kishi na hauka a gidan mijinta ba. Allah yayi ƙarewar aurenne dan ku maza in kuka auro wata macen kukan juyama wata baya na wani lokaci kafin ku gama shan romonta. Abunda Hadiza bata da ilimi akai kenan shi yasa aurenta ya mutu a wannan gaɓar. Amman Nagode da wannan furuci naka" Ta ƙarashe maganar tana shessheƙar kuka mikewa tsaye tayi tana shirin barin ɗakin. Malam yayi carab ya cafe hannunta. Tayi sauri ta runtse idanunta tare da fashewa da wani irin kuka mai ɗaci. A wannan daren Baba Magaji ya sha rarrashi da ban baki. Dan har kuɗi ya debo da baisan iyakarshi ba ya bata da safe kafin ta koma ɓarayinta. A haka soyayyar Gwadabe da ƴan matanshi biyu taci gaba da kasancewa. Ko wacce cikinsu na ƙoƙarin ganin ta nuna bajintarta. Danma ba wacce ta san da zaman ƴar uwarta, iyaye sun bar zancan a tsakaninsu. Domin shi Baba Magaji a ganinshi Gwadabe ai bazai haɗe mata biyu a lokacin guda ya aura ba, dole da ɗaya za'a soma. Ta ɓangaren neman Gwadabe kuwa, Allah yasanya mishi albarka a harkar neman. Dan yana da ido sosai na ganin zinariya. A zuwanshi har ya samu zinariya sau biyu, kuma ba laifi madaidaita ne. Hakanne ya bashi damar yi ma Babala aike, ita da Bara'u abokinshi na amana. Da yamma lis yau su Gwadabe suka shigo gidan, sun shawo gajiya sosai. Harda ƴar ledar kayan kwalliya a hannun Gwadabe. Ɓarayinsu suka wuce dai kamar kullum, sai da su kai wanka suka sake kayan jikinsu. Yayi daidai da lokacin Sallah sai suka wuce kofar gida dan gabatar da sallah. Ta ɓangaren Hadiza kuma tayi kwalliyarta me ƙayatarwa sai ƙamshi take faman zabgawa, ga abinci ta ajjiye da kwanukan zubawa, shigowar su Gwadabe kawai take jira. Baba Fhatsima kuma tana zaune daga gefe tana jin wani shiri da ake gabatarwa a gidan rediyo hankalinta yana wajen shirin. Amman idanunta na kan Hadiza wacce tun ɗazu sai gyare_gyaren gashin kanta data bazoshi ya sauka kafaɗarta take yi. Irin wannan ganɗoki ko a aurenta na fari ma bata yishi ba, duk da shima wancan auren Malam ne ya haɗashi almajirinshi ne mijin. "Hadiza sai nake ganin kamar kin zafafa soyayyar da kike ma Gwadabe. Kibi a hankali kinsan halin maza da karya ma mace zuchiya. Ƙila ma bake kaɗai bace a ranshi" Ƙur ta zuba mata idanu tana karantar yanayinta, dama ta soko zancanne taji irin amsar da zata bata. Dan tana son auna kishinta da Malam yake ta ikirarin ita ta biyo" Ƙasa tayi da kanta, lokaci guda sai ta jagule har idanunta ya kawo ruwan hawaye. "Baba abinda ya faru a baya kuskurene wanda bana mafarkin ya sake faruwa dani a gaba. Nasan an yi mun laifi, amman nima na nuna rashin hakurina ƙarara. Wallahi a lokacin da Tsalha ya dinga nuna mun ni ba cikakkiyar mace bace, sai da yayi amarya ya gane kanshi. Banyi tunanin a daren zan rayu ba, wani abune yake dannemun harshena izuwa moƙoshina. Baba ina da kishi mai yawa, anata cewa wai ke na biyo. Ni kuma in sha Allah zanyi koyi da salon kishinki, da dabarun kissarki ta hanyar gina babban matsayi a zuchiyar Gwadabe. Ta yadda ko mata ɗari zai auro bai isa ya haɗemu a matsayin abu guda ba" Kuka ta fashe dashi mai ciwo. MRS BUKHARI Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Jfn7qq4nyMm0prVhnhfVZK *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Jfn7qq4nyMm0prVhnhfVZK *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE LITTAFI NA BIYU 4 Baba Fhatsima ta dubeta a tsanake tace. "Shikenan ni da kaina zan kwatanta miki yada zaki zauna daram ki wuce wulaƙanci a zuchiyar ɗa namiji. Hadiza a lokacin da Malam yace zai ƙaro aure sai da na kwanta jinya. Amman sabida kirsa irin tamu ta mata ni na haɗa akwatin da Malam ya kaima Asshi. Kuɗin dana samu a hannun malam bana wasa bane. Zuchiya kullum ciwo da zafi suke yi mun Hadiza. Wallahi inna kalli Malam sai inji kamar in ɗura mishi zagi. Amman wallahi ko ɓacin rai baya iya ganewa a fuskata. Horon da nayi mishi na ƙauracema shinfiɗarshine, tunda ya raina iyawata, sai da nasa da kanshi ya gane mahimmancina da kuma banbancina. Duk da ina fishi dashi, saina dukufa shan magunguna ingantattu, musamman tukuɗi da gumbar matan Kanuri da tsuminsu, da shayin su na musamman. Na dinga gyaran kaina dan sake kankaro mutuncin kaina. Ni kishina bana ayi zagi ko bankaura bane. Da duk tsufana Malam har gobe yana mararina Hadiza. Sallamar su Gwadabe ce ta katse wannan tattaunawa wanda nasan ba Hadiza kaɗai ke karuwa da'ita ba, harda masu karatu. Saurin share hawayenta tayi, wanda karab a idanun Gwadabe. "Baba yinwa" Cewar Auwala wanda baya jurar yinwa. Dariya duk aka saka mishi. Baba Fhatsima tace. "Ai kai wacce zata aureka ba zaka barta ta huta da ɗaura sanwa ba" Saida ya cusa tuwo loma babba a bakinshi, tun kafin Mammada ya gama zuba musu, kana yace. "Tabb ai ni tun da jimawa tasan Yaya nake. Kullum naje saita kawo mun shayi da cukui, wataran harda abinci fa." Mammada yace. "Bayan uban abincin da kake take cikinka dashi kafin ka tafi? Shi yasa cikinka kullum yake ƙara girma. Baba yau daya zarme rijiyar haƙon zinariya da ƙyar aka zaroshi tsabar ƙiba fa" Duka Auwala ya kai mishi, yai maza ya matsa kusa da Gwadabe wanda shi kuma hankalinshi na kan gimbiya Hadiza da yaga tana cikin rashin walwala. Baba Fhatsima tayi Dariya tace. "Duk ai ya kusa karewa gini kam gobe za'a soma an kawo bulo da yashi, an yi ginshiƙi. Aikin ba wani daɗewa zaiyi ba tunda an riga da an tanaji kudin aikin. Duk kuyi aurenku nima na huta" Gwadabe yace. "Ai Baba kila fa Auwala ya dinga zamowa cin abinci ɗakinki, baya zage ya kwashi girki a gaban Amarya haka ba" haka dai sukaita raha a tsakaninsu kamar yadda suka saba a koda yaushe. Ana cikin haka Yaya Tasi'u shima ya shigo akayi hirar dashi. Kiran sallar isha ne ya fasa taron. Da Gwadabe ya tashi fita sai ya ajjiye ledar kayan kwalliyar da ya siyo ma Hadiza a gefen ƙafarta ya fita. "Tashi kiyi Sallah kafin Gwadabe ya kiraki zance, dan zancanku ba ɗaga ƙafa. Yaran zamani kome kuke cewa in kunje wajen zancen oho. Zance ai sai su Ine yanzu dai duk ya ƙare." Hadiza tayi murmushi tace. "Gobe ma mu kayi da Anty Badi'a zamu je gidajensu mu ganosu, tun bayan biki mu ta ɓangarenmu babu wanda yaje. Shekaran jiya Sauma'iyya suka je gidan Hafsatu." "Daga gidan mijinta taje, ke yaya akayi kika san taje? Tsegumi" Dariya Hadiza tayi tace. "Baba asshi ce naji tana faɗama Amaryar Malam. Wai Hafsatu ta aiko mata da kuɗi harda soyayyun zabbi" Harara Baba Fhatsima ta doka ma Hadiza ba shiri ta tada kabbarar sallah. Dan babu abinda Baba Fhatsima ta tsana irin gutsiri tsoma" Hadiza tana kan sallayar bata tashi ba Gwadabe ya aiki yaron Amaryar Malam yayi kiranta. Sai da ta kuma gyare_gyaren kwalliyarta kafin ta fita. Baba Fhatsima tana jimantama Hadiza ranar da zata ji labarin bada ita kaɗai Gwadabe yake soyayya ba, kuma akwai yiwuwar ba ma ita kaɗai zai aura ba. Ko da ba'a hade bikin ba, tasan babu wani nisa a tsakani. Fitowa tayi tsakar gidan tana busa ƙamshi. Amaryar Malam da taci kwalliyarta na zuwa turaka ta bushe da dariya, dama can basa shiri sam da Hadiza. Dan bama su wuce sa'anni ba. Ko kallonsu batayi ba. Harfa ta sha kwanar ɓarayin su Gwadabe ta jiyo Baba Asshi na cewa da Suwaiba. "Sabida tsabar tayi bandarine fa Malam ya tafi ya ɗauko ɗan ƙanwarshi dan ya haɗasu. Ƙanwar tashi ma da bata da mutunci. Ni dai na gode Allah in Fhatsima ta fini da soyayyar miji, da ɗa mai arziki. Bata fini a surukai ba. Dan masu arzikin gaske ƴaƴana suke aure. Itako Hadiza gidan da za'a sakata ubanta nema ya bayar" karab a kunnen Hadiza, karab kuma a kunnen Baba Fhatsima. Dukkansu kai suka girgiza kawai. Hadiza tayi shigewarta ciki. A bakin dakalin ƙofar ɗakinsu yake zaune. Ga hasken lantarki tanwar ya haske ko'ina. Gardawan malam su biyar suna wajen suna wankin suturunsu, sai Sabitu dake tsaye a ƙofar ɗakinsu kawai dan babu dai Abinda yake yi. Kwana biyunanne ya tsiri yin hakan a daidai lokacin da Gwadabe zai fito ya zauna domun ganawa da Hadiza. Tun daga nesa Gwadabe yake ƙarema Hadiza kallo. Zani daya gani ɗaure a jikinta sai yake ganin kamar iyabo ce ke tawowa, dan Iyabo ta ƙware wajen iya ɗaurin zani sosai, takanyi matuƙar kyau da zani, ƙibarta na daga cikin abinda ke sa ruhinshi ke fisgarshi akan son Iyabo. Isowar Hadiza ce tasa ya dawo hayyacinshi. Zama tayi gefenshi sosai. "Barkanka da wannan lokacin angon Hadiza mujin mace ɗaya tilo." Murmushi yayi mata kawai, a kullum in ta kirashi da mijin mace ɗaya tilo sai yaji faɗuwar gaba, haka ƙanwar tamu take yawan ce mishi. "Mijina ni ni kaɗai. Babu wata mace data isa ta rabeka" Da sunyi mishi irin furucinnan sai yaji hankalinshi ya tashi a madadin ya samu nutsuwar kalaminsu. Anya bai cutar da zukatan ƴan matan ba kuwa, lokaci baiyi da zai bayyana musu gaskiya ba kuwa? To wai in ya zayyana musu gaskiya du suka gujeshi ya zaiyi da kunyar waɗanda yake ganin darajarsu a jikin ƴan matan? In kuma suka ritsashi suka ce sai dai ya zaɓi ɗaya, Yaya wacce aka ce tayi haƙuri zata yi? Haƙiƙa yayi kuskure mafi girma da rinjaye, awannan tunanin kamata yayi tun farko zaiyi shi, ba yanzu da wankin hula ya riga ya kaishi dare ba." "Wai tunanin me kake yi ne Yaya tun ɗazu inata magana fa, bakace komai ba" Ya tsinkayi shagwaɓaɓɓiyar Muryar Hadiza, wanda tasa saida tsigar jikinshi ta tashi, dan wannan yana daga cikin sabon salon da take son fitowa dashi dan mallakar zuchiyar Gwadabe. "Akwai muhimmiyar maganar da nake son mu yi ni dake. Hadiza banaso ki fassarani da ko wacce iriyar mummunar fassara, ina cikin tsaka mai wuyar fita ne, abinda yasa abinda ya faru ya farun kenan." Shiru tayi tana kallonshi da ƙananun idanunta waɗanda gashi sukaima rumfa. Bayan ta ja numfashi na daƙiƙa sai tace. "Ina saurarenka, zanyi maka shari'ar gaskiya da gaskiya. Faɗamun matsalar dan tuni fuskarka ta nuna matsala zaka faɗa mun" Shiru yayi yana shafan sumarshi kanshi. "Hadiza ba da ke kaɗai nake soyayya ba. Akwai ƙanwar abokina Tamu da ya bani tun kafin in tawo Nijer " Darara dam_dam_dam gabanta yai mummunan tsinkewar daya tunkudo ruwan hawaye nan take suka soma shatata a idanunta. Duk da haka tace. "Dan Allah kace dani wasane, kar kayi amfani da kishin da akace maka shi yai sanadiyyar mutuwan aurena ya zamema logo. Na roƙeka karka yaudari zuchiyar data saba da rayuwa da sonka." Take hankalin Gwadabe ya kai ƙololuwar tashi, dan bai taɓa tunanin Hadiza zata ɗauki wannan lamarin a yanda ta ɗauka yanzu ba. Da ƙyar ya samu kuzarin ce Mata. "Wallahi da gaske nake yi Hadiza. Kafin in tawo nan na riga dana amshi soyayyarta. To kuma da nazo nan sai Baba Magaji yace in zaɓi mace a cikin ƴaƴanshi in aura, amman sai yace yafi mun sha'awarki" "Kenan ba sona kake yi ba, Malam kai ma biyayya? Shikenan ni na hakura kaje ka aureta" Tana gama faɗar haka ta mike fu ta bar barayin. Yayi yinƙurin tareta sai Auwala da shigowarshi barayin kenan ta gefenshi ma Hadiza ta raba ya dakatar da Gwadabe bisa dole ya tsaya." "Koma me ya haɗaku kyaleta ta huce, su mata a cikin irin wannan halin baka iyawa dasu sam." Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke tare da lumshe idanunshi. "Auwala laifi nayi mata. Tana da dalilin yin fishi dani. Laifinane, dan Allah ka bita ka bata baki a madadina" "To wannan ma dabarace. Kai jeka bari in shawo maka kanta ka koma ciki ka jirani." Gwadabe na shiga ɗaki kiran Shafa na shigowa wayarshi. Jiki a mace ya ɗaga wayar, itama yayi mata duk bayanin da yaima Hadiza. Ƙit ta kashe wayarta, ko da ya kuma kira sai yaji a kashe ma wayar baki ɗaya. Dafe kanshi yayi bakinshi na ɗaci, damuwa duk ta haɗu ta dameshi. Hadiza. Da sauri ta shiga ɗakinsu har tana cin karo da Ine wacce suke shirin fita ita da mijinta sun kawo ma Baba Fhatsima ziyara irin ta godiya da angwaye suke yi. Ganin mijin ƙanwarta yasa tai saurin share hawayen dake bin gefen fuskarta. "Ango ka sha ƙamshi kune a tafe da daddarennan? Mu da muke shirin kawo muku ziyara" A ladabce ya gaishe da Hadiza yana yi yana sosa kanshi. "In kin gama kya same ni a waje ni kam" Yace da Ine wanda hankalinta yake kan Hadiza. "Yaya Hadiza nifa fishi nake yi wallahi. Tunda kuka kaini ba wanda ya sake leƙoni ma" Ta faɗa a karaye yayinda Hadiza take kallonta da halamar tuhuma. Ganin hawaye na neman ɓallewa a idanun ƙanwar tata ne ya tabbbatar mata tana cikin damuwa, ko kuma kewar gida." "Ki sha kuruminki dama gobe zamu je gidanki ni da Anty Badi'a. Yanzu dai kije ki samu mijinki karki barshi yaita jira" Ine tace. "Bamu shiga cikin gidanba ma, yanzu dai zamu zazzagaya, amman munje ɓarayin su Yaya Tasi'u." Fitarta shigowar Auwala yana kwaɗama Hadiza dake shirin zama kira. Shigowa yayi ranshi a matuƙar ɓace. "Ke meye ya haɗaki da Gwadabe, da har yake kiranki kina ƙin tsaiwa? Ki sani wanki ne Gwadabe, kuma mahaifiyarshi ƙauna take ga Malam." Hadiza najin wannan sababi na Auwala sai ta saki rushin kuka tana faɗin "Ni wallahi na fasa auren. Yaje can ya auri ƙanwar abokinshi. Ai ba sona yake yi ba. Malam ne ya cusani wajenshi" Duka Auwala ya kawo mata. Baba Fhatsima dake zaune tana kallonsu tace. "Bita a hankali Auwala. Zo zauna inji meke faruwa haka uhm?" Zama Auwala yayi a ƙasa, yana dokama Hafiza harara. "Ki buɗe baki kiyi mun bayani Hadiza. Menene ya haɗaki da yaiyen naki?" Hadiza ta kwashe yanda Gwadabe ya faɗa mata ta sanar ma Baba Fhatsima. Tsaki dogo Auwala ya ja yace. "Ni nama ɗauka wani muhimmin abune yanda naga Gwadabe duk ya damu. To sai me dan ba da ke kaɗai yake soyayya ba, dama cewa akayi dan ke aka halicci Gwadabe ke ke kaɗai? Baba kinji fa abinda take cewa, wannan baƙin kishin nata ne yasa ta tsallake yaranta ta dawo gida. Tana da aiki ja matsawar irin wannan ƙazamin kishin bai fita a ranta ba." Shiru Baba Fhatsima tayi, tana sauraren ɓaɓatun Auwala, da sautin kukan Hadiza. Ajjiyar zuchiya ta sauke kana tace. "Hadiza kina nufin ba zaki taɓa zama da kishiya ba ko me kike nufi? Bar ganin ina goyon bayanki Hadiza, ai in dai wai ke bazaki zauna da kishiya bane, to ya fiye miki sauƙi ki ƙare rayuwarki a gidan mahaifinki. Dani da Malam mun san bake kaɗai Gwadabe yake nema ba, kuma a haka muka ji yafi miki ki aureshi. Dan Gwadabe yarone mai hankali da kunya. Ke dai kiyi fatan kasancewa uwar gida a gidanshi kawai. Kai Auwala tashi yi tafiyarka, ka kuma cema Gwadabe ya kwantar da hankalinshi Hadiza mu muka bashi ita, duk duniya in banda ƙaddara babu wanda ya isa soke batun aurennan. " Tashi Auwala yayi ya dubi Hadiza yace. "Yara basu ajjiye komai ba sai sakarci. Ni zan so ma Malam ya soma aura mishi waccan ɗin kafin ita. Gashi ita ƴar birni wayayya da'ita, kuma hankalinshi take janyewa sosai. Maza ki tsaya kallon ruwa kwaɗo yayi miki ƙafa" Baba Fhatsima ta daki ƙafafun Auwala dake son tunzura Hadiza. "Ja'irin yaro, fice ka bamu waje" Ta faɗa cikin sigar wasa, fita yayi yana sake kambaba yanda budurwar Gwadabe take kulawa dashi a waya. Kuma duk dan ya tunzura zuchiyar Hadiza ne. Ai kuwa yaci nasara dan take zazzaɓi me zafi ya luluɓeta, sai hawaye idanunta yake fitarwa" Harara Baba Fhatsima ta doka mata tare da cewa. "Shashasha maza dai ya gane kishi shine logonki kiga in baki faɗi ƙasa warwas ba. Ba'a ƙarin aure ni Malam yayi mun har kishiyoyi uku? Da banyi haƙuri ba ke kina ganin zan kai haka ne? Ai mace a gidan aure da jarumta akeson ganinta Hadiza. Dan Gwadabe ba ke kaɗai yake nema ba, ba hujja bace na cewa ke kin fasa aurenshi ba. Ai kina gani a cikin gidannan dama dariya suke yi ta mana. Ko baki ji Abinda suke cewa bane ɗazu da zaki je wajen Gwadaben? Ai kinji sarai. Maza dai ki ma kan ki shaidar da babu me iya goge miki ita na zafin kishi. Ni kinga tafiyata Malam na son ganinmu dukka a turakarshi, Allah dai yasa lafiya. Dan malam bai fiye haɗe kan matanshi ya tattauna dasu baki ɗaya ba, yafi gane ya tattauna da kowacce ranar girkinta" Tana gama faɗar haka ta sa kai ta fice ta bar Hadiza da jinyar zuchiya. Yayinda maganganun Auwala suka shiga yi mata amsa kuuwa. "Ni inata wahalar da kaina na son ganin na burgeshi. Sai gashi ashe wata a waya kawai take jaye mai hankalinshi. Ni Hadiza zan iya zaman kishi a karo na biyu kuwa? Wallahi nasan mata ƴan uwana da yawa ba zasui mun uziri ba Wasu ma zagina zasu yi. Amman Ubangijin da yayi ni, ya yiku. Shi ya banbanta zuchiyiyoyinmu. Wata abinda tata zuchiyar ta ɗauke, wata in akace sai zuchiyarta ta ɗauke wallahi mutuwa za tayi. Ni Hadiza macece mai mugun kishi mai zafi, nifa ko baiwace na fi son ace tawace ni kaɗai babu mai irinta. Kishi ni shine raunina nasan ko wacce mace da irin rauninta." Baba Fhatsima" Lallai hausawa sun yi gaskiya da suke cewa magaji mafiyi. Ita kanta Baba Fhatsima tana mamakin yanda Hadiza ta xama kwafinta a kishi. Komansu iri ɗaya ne ta ɓangaren kishi babu inda ta barota saima finta da tayi. Ita kanta da ba dan ta kai zuchiyarta nesa ba, da kuma tunanin goben yaranta ba, da a lokacin da malam zai ƙaro Aure da tuni ta bar auren kwata_kwata. Har gobe zuchiyata tana azabtuwa ainun da zaman kishin da Malam ya haɗata yi da sauran matanshi. Duk da tasan cewar ita da Tasi'u sune fitulun dake haska gidan malam, hakan bai hanata kishi ba. Iya rigima Malam yake kiranta a duk sanda ta murɗa kambun kishinta ta juya mishi baya. Ajjiyar zuchiya ta sauke a daidai shigarta ɓarayin da turakar Malam take. A zuchiyarta take roƙama Hadiza Allah ya bata haƙuri da juriya. Ɗayar zuchiyar tata tana cike da tausayin Hadiza a bisa dakon nauyin kishi da zata ɗauka na iya tsawon rayuwar duniyarta. Da sallama ta shiga falon na malam, yana zaune a kujera mai cin mutum uku Amaryar Malam tana gefenshi tana kiciniyar cire mishi babbar rigarshi. Baba Fhatsima ta haɗiye wani yawu mai kauri, tare da yin wuf ta yi ƙasa da idandunanta. Kunya da nauyin Fhatsima suka kama malam. Cikin dibibicewar data mugun ƙular da Amaryar Malam yace. "Uwar gida sarautar mata, farar mace alkyabbar mata, zo ki zauna Fatsima" Ɗan siririn ɓoyayyen tsakin da a iya kunnen Baba Fhatsima ya sauka Amaryar Malam tayi. Kujerar gabaki ɗaya ta sauka ta barma malam da Baba Fhatsima, ta koma kujera mai cin mutum guda ta kumbura tai suntum. Murmushin takaici Baba Fhatsima tayi, a zuchiyarta tace. "In banda maza da faɗuwar girma ni Fatsima da yaushe zan haɗa gado da yarinya ƴar cikina? Amman su maza basa ko jin kunya, da nauyin manyan yaransu. Wacce iriyar taɓarace Malam bai yi ba lokacin da ludayin Amaryarshi ke kan dawo? Murmushi ta kuma yi mai cike da fassarori da dama. "amarya ina ganin sai kin tashi kin kirawo mun Asshi, da Suwaiba Lokaci yana ƙurewa ya kamata ace sun hallara" Ba dan ranta yaso ba ta fita ta bar Malam daga shi sai Baba Fhatsima ba. Tana fita Malam ya dubeta yace. "Fatsima bakya tsufa ke dai. Wazai ga Tasi'u yace ke kika haifeshi?" "Hmm Malam Baka rabo da daɗin baki, koma kince borin kunya" Da Malam da ita da tai maganar suka kwashe da Dariya. Shi yana dariyar yanda akayi ta ɗagoshi. Ita tana mai dariyar kaji kunya. A haka matan Malam suka shigo suka iskesu. "Au aini naga kamar Amaryar Malam itace da girki ko? In ba ɓatan lissafi nayi ba. Ta faɗa tana kallon Amaryar Malam data cika tana shirin fashewa. Suwaiba ta taɓe bakinta tace. "Girkinta ne, kin mance ita ta wuni tana hidimar yara?" Malam ne ya dakatar dasu ta hanyar cewa. "Yanzu zaku zauna kuji dalilin kiranne ko kuwa zaku tsaya bin ƙididdigar waye me kwana waye marar kwana ne. Wai shin me yasa ke Asshi baki da aikin daya shige na ta da tarzoma ko da yaushe?" Zama ko wacce tayi a kujera. Amaryar Malam ta je ta zauna a kusa daf da Malam. Bai dai ce da'ita uffan ba. Takaddu dunkulallu ya ciro daga aljihun rigarshi ya zube a ƙasa. "Ko wacce ta ɗauki ɗaya ta riƙe a hannunta kafin in gama bayani sai ku buɗe. Sai da kowacce cikinsu ta ɗauka sannan Baba Fhatsima ta ɗauka a ƙarshe. Malam yace. "To wannan ƙuri'ace nayi muku kamar dai yadda nake yi a ko wacce tafiya in ta taso mun. Kuma tunda nake yin wannan ƙuri'ar duk wacce ta ɗauki tafiya bana sakewa da'ita nake tafiya. To a wannan karonma wata tafiyace ta taso babba a gabana ta banbanta da duk tafiye_tafiyen dana saba yi a baya. Naba ko wacce dama ta buɗe takaddarta duk wacce ta ɗauki tafiya to Allah ya ciyar da'ita. Sannan ku sani babu zalunci ko son kai a cikin wannan lamarin Allah shine shaidata. Bismillah ko wacce ta buɗe. Nan da nan ko wacce ta shiga kiciniyar buɗe takaddarta tare da zabarin ganin ta ɗauki tafiya Domin tafiya da malam ana samu alkhairi sosai, kuma macce tana samun lokacin kanta dana mijin nata, soyayya ake darza tsantsa. Cikin sa'a Baba Fhatsima ta samu tafiya. Har cikin ƙasan ranta tayi farin ciki sosai, dan ta jima sosai rabon da ta samu damar tafiya tare da Malam. Kuma a halin yanzu tana cikin yarda dashi. Baba Asshi tafiyar da yayi na ƙarshe wacce ba'ayi wata ba sai yanzu, tare da'ita akaje. Amaryar Malam kuwa sai da ta samu takaddar tafiya sau huɗu a jere ras, Suwaiba ta samu sau biyu a tare. Wannan karon kuma Allah ya ciyar da Baba Fhatsima. "Malam nice na samu tafiya" Bai san sanda murmushi ya subce mishi, farin ciki ya bayyana s fuskarshi ba. Malam har tsaiwar dare yayi kan Allah ya dafa mishi Baba Fhatsima ta samu wannan takadda ta aminci. Kawar da kai Baba Asshi tayi gefe, tare da taɓe bakinta. Malam kuwa yace. "Masha Allah dama kina da paspo ta kwana gidan sauƙi sabida haka ki soma shirin keta hazo" murmushi Baba Fhatsima tayi mai cike da danƙararriyar soyayyar Malam da take ta farfaɗowa. "Allah ya nuna mana lokacin malam. In ka bani dama sai in koma ɓarayina" Kai ya gyaɗa. "Ki isa cikin aminci Fatsima uwar gida ran gida" Ai fitar Baba Fhatsima sai tarzoma ta tashi, daga ƙarshe dai fatattakarsu Malam yayi. Amaryar Malam dake da kwana itama ta bisu tana kuka wai ta yafe kwanan ma baki ɗaya. A wannan daren zukata da yawa a cikin tunani suka kwana, ko wanne da abunda yake tubkewa da warwarewa haka garin ya waye kamar yadda aka saba. Gwadabe:. Tun asuba yake kiran wayar Shafa amman wayar har zuwa lokacin a rufe take. Gashi yana son zuwa ganin Hadiza yaga ya ta kwana. Duk da Auwala ya kwantar mishi da hankali a daren jiya. Tashi yayi jiki a saɓule ya nufi cikin gidan. Yau matan Malam babu wanda ya amsa gaisuwar su Auwala ma balle kuma Gwadabe wanda yazo dandalar arziki. Sai Baba Fhatsima ce dake zaune a dokin ƙofa tana siyan lalle da gishirin lalle akan wata yarinya tace. "Gwadabe yau makara kayi ne sai yanzu ka samu shigowa?" Da biyayya ya zube ya gaisheta, ta amsa cike da fara'a. "Ka shiga Hadiza na ciki, da zazzaɓi ta kwana, likita ma Matar wanku zata kaita" Kai ya kuma saukewa harda sosa kanshi. "Subhanallaah Allah ya bata lafiya, bari in dubata" Ya faɗa da kunya. Shiga yayi ya samu Hadiza a zaune tana shan kunu. Ƙurama juna idanu su kayi na daƙiƙu. Ita ta rigashi sauke ido. "Ina kwana Yaya Gwadabe?" Bai samu damar amsawa ba, waje ya samu ya zauna a ƙasa ƙur idanshi a kanta. "Ina roƙon Allah yasa ba maganata ta jiya bace sanadiyyar ciwonnan naki ba Hadiza?" Bai jira ta amsa shi ba dan bai tambayeta yana nufin saita amsaba ya ɗaura da faɗin. "Wallahi ba dan Baba magaji ya tozartaki ko ya ƙasƙantar da darajarki bane yasa yai miki zaɓin Gwadabe ba. Nima ba dan tayin da yaimun bane yasa na amsheki ba face kin yi mun kuma naji zan iya rayuwar aure dake. Yanayinki da zubinki yana mun kama da na matata Iyabo sosai. Ki fahimceni auren zumunci cike yake da tarin hikimomi. Itama fa bawai ina nufin bana sonta bane A'a itama inai mata kalar nata son daban. Hatta tsohuwar matata gurbinta shine a ƙasan zuchiyata. Ki kwantar da hankalinki kinji?" Tunda ya soma magana zuchiyarta ke lugude. Musamman da taji matsayin da Iyabo ta wawashe a rayuwar Gwadabe. Sai Allah ya sadamu ranar Monday da izinin Allah danjin yadda zata kaya. Ki faɗi abinda kika ɗauka na darasi a wannan labarin duk da bamu yi nisa ba. https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE BOOK 2 5 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* _Assalamu Alaikum barkanmu da juma'a. Iyabo tana godiya a bisa karɓar labarinta da kukayi hannu bibbiyu_ Lokaci ɗaya taji kishin Iyabo ya soki murfin zuchiyarta fiye da kishin wacce za a haɗasu zaman kishin na gasken_gasken. Bata sami zarafin furta mishi kalma ba Auwala da Anty Badi'a suka shigo a tare. "Hadiza in kin shirya muje Yayanku ya rage mana hanya ko?." " to" Ta furta tana kallon Gwadabe, wani irin kallo daya kasa fahimtar fassararshi. A kunyace ya gaishe da Anty Badi'a, ta amsa cike da kulawa. "Gwadabe maza muje Mammada na jiranmu kasan fa yau muna da aiki." Cewar Auwala kenan. Kafin ma ya miƙe Malam Magaji ya iso dokin kofar yana faɗin. "Yarannan har yanzu basu wuce aikin ba, Auwala me kuke yi a ƙunshe a ƙurya haka?" Da sauri suka fito, sumi_sumi sukai ma iyayen sallama suka fice a gidan. Cikin sa'a Gwadabe ya gwada sake kiran layin Shafa ya samu a buɗe. Sai dai harta gama kuka ta tsinke ba a ɗaga ba. Yana sauke wayar a kunnenshi sai ga kiran Tamu ya shigo. "Abokina yau kaine da kira sassafe haka, ya kwanan iyalin kuma?' Cewar Gwadabe daya tari numfashin abokin nashi ta hanyar rigashi magana. Ajjiyar zuchiya ya sauke yace. "Tun jiya Ayashe ta sanar dani Shafa nata faman kuka ta kulle kanta a ɗaki. Ko da aka wayi safiyar yau taƙi cin abinci, taƙi zuwa wajen aiki. Shine nasa ita Ayashe tai kiranta dan inji menene. To ta dai ƙi yin magana ma, bansan ko kana da masaniya akan kukan ba, kasan yarannan fa da zafafawa akan soyayya, dan naga ta ɗauki lamarinka da girma. Kasan mata da surutu ina jin labaranka sosai ta bakin Ayashe" Jim Gwadabe yayi kawai yana mamakin halin da Shafa da Hadiza suka shiga a kanshi, ya ɗan shafo ɗan siririn hancinshi tare da shiga zancan zuchi. "Ohh ni Gwadabe ni ba kyau mai suna kyau ba, ni ba tsayi ba, ga tumbi, ga ƙaton kai. Amman akaina waɗannan matan suke shiga damuwa haka? Dama_dama Iyabo na cancanci ta soni, duba da yanda tasha naci a wajena, da irin yanda na jajirce kan soyayyarta. Amman waɗannan haɗani dasu dukka akayi, bawai ni nace ina sonsu ba." "Kana jina kayi banza dani Gwadabe ko network ne, ko ko dai wani rashin kunya Shafa tayi maka?" Tamu ya tsinke mishi zaren zantuttukam zuchin shi. Da sauri yace. "Kai kasan komai Tamu akan Hadiza da Baba Magaji ya bani bayan na baro najeriyane. To ita Hadiza bata san da zaman Shafa ba, kamar yadda Shafa bata san da zaman Hadiza ba." Nan dai ya kwashe labarin duk yadda ta kasance musu a jiyan. Tsaki Tamu yayi kawai tare da cewar. "Shirmen banza harma ka tunzurani ƙila saina zaneta ma. Yanzu akan wannan maganar ne duk ta takure kanta?" "Kul wallahi kar ka soma dukan mun mata ni dai na faɗa maka dan ubanka" Dariya suka yi Tamu yace. "Wannan siriki kwai fitsararren maras kunya" Dariya suka sake sawa, kafin Tamu yace. "Yaushe zaka shigo mana najeriyar ne Gwadabe, ka gujemu. Ko dai har yanzu damuwar rashin Iyabo ne ya hanaka zuwa? Mu kuma cike muke da kewarka, ko babu komai ya kamata kazo kaga yara" Gwadabe yaji wata kewa ta kamashi, take yaji yana sha'awa da son ganin abokan nashi da ma yaranshi. "Tamu zan zo zuwa ƙarshen wannan watan da muke ciki, kaga yau wata yayi goma biyar, yana kaiwa ƙarshe zan zo in duba ku. Ya yaran?" "Yara kowa lafiya lau sunata karatunsu hankali kwance. Toye ma dana shiga ƙauye naga yayi noman masara shi da yaron Bara'u baka ga yanda masarar tai kyau ba. Na lura yaron yana da mai da kai akan abinda yake gabanshi, shi kanshi Bara'u ya yaba" Sun jima suna hirarsu ta abokai kafin daga bisani su kai sallama. Ko da yaje wajen aiki daya fito cikin ramin haƙar zinariyar dan hutu sai ya kira lambar Shafa, bata shiga ma baki ɗaya. Da ƙyar ya samu dai ta shiga, kuma yaci sa'a aka ɗauka. Daga nan zancan fishi ya ƙare, bayan ƴan bayanai daya yi mata, da kuma kalamin kwantar da rai, sai suka balle da hirar soyayya, wanda rabi da kwatan hirar Shafa ke yinta, shi dai yana dai ƙarfafa mata guiwa ne. Bayan sun yi sallama ya kira Hadiza ma yaji yaya jikin nata tare da ɗan taɓa hirar da rabinta da kwatanta labarin zafin da taji a zuchiyarta ne, shi dai aka barshi da aikin rarrashi. Jigum ya zauna yayi tagumi bayan gama wayarshi da Hadiza. Kanshi ya ɗauki caji ainun. Harga Allah shi dai bazai iya gane yana son su Hadiza ne, ko kuma yana kallon darajar waɗanda sukai mishi tayinsu ne ba. Domin mace ɗaya tilo Iyabo itace a zuchiyarshi abadan. Yasan abune mai wuya dawowar Iyabo cikin rayuwarshi. Yana fatan inya shiga Najeriya Allah ya haɗa fuskokinsu ko da a hanya ne. Yana kuma da burin son ƴaƴanshi su yi rayuwa a gefenshi damin ya ɗauke musu raɗaɗin maraicin uwa a rayuwarsu. Mammada ne ya dafa kafaɗarshi, yana zaune a gefenshi shi bai ko ji tawowar tashi bama. Abinci ya miƙa mishi, garau_garau irinta leburori irinsu, yasa hannu ya amsa. "Menene Gwadabe, kaddai batun Hadiza ne duk yabi ya dameka?" "A'a wallahi Mammada tunanin rayuwa kawai nake yi da rashin daɗin aikinnan, tare da tunanin yarana da basa kusa dani anan" Ɗan murmusawa yayi, sai da ya ciko garsu_garau a cokali ya danna a bakinshi dam kafin yace. "Wannan ai mai sauƙine Gwadabe, kai da kake jarumi me auren mata biyu, ai zasu riƙe maka yaranka wannan bama wata matsala bace" Abincinshi yaci gaba da dannawa a baki bashi da damuwar komai. Sai Gwadabe yaji dama ace shine Mammada da yaji daɗi. Wunin wannan rana da tunanin Iyabo da yaransu Gwadabe ya wuni. Yayi ƙoƙarin samun layin Bara'u ma dan ya sanar mishi da batun zuwanshi, amman dai basu sami damar jin juna ba. Kamar dai yadda aka saba bayan isha Gwadabe ya aiki yara su kai mishi kiran Hadiza. Yana zaune a saman dakali tazo ta sameshi, bayan sun gaisa yayi mata ya jiki, sai shiru ya biyo baya. Dukkansu a cikin tarawa da ɗabewa suke. Sai dai tunaninsu ya sha banban dana juna. "Menene ya dameka wanda harya kasa ɓoyuwa akan fuskar taka, ko baka samu damar jin muryar Shafa bane?" Ɗagowa yayi suka haɗa idanu. Ɗan gajeren murmushi yayi mata tare da cewa. "Babu mamaki dan naji sunan Shafa raɗau a bakin ki, tunda Malam yasan sunan. Yaya jikin naki da sauƙi, kuma kinsha magungunan da suka baki? Ya jero mata tambayoyin da yake tunanin zasu jaye hankalinta daga barin batun Shafa. Amman sai ta jefo mishi wata tambayar da cewa. "Ni ko zan so ganin tsohuwar matarka ko da a hotone domin inga da abinda tafi sauran mata" Ta ƙarashe maganar da taɓe bakinta. Anan ne taga ya gintse fuskarshi dukkan annurunshi ya dakata. "Kar ki kuma kawo maganar Iyabo anan wajen. Ki tsaya dai iyakar matsayinki da kike dashi a zuchiyata. Batun ita kanta Shafa ki shafe shi a kan ki, ni dake mu tattauna akan iyakar abinda yake gabanmu. Kuma ko ita Shafa in tayi mun magana a kan ki, ko Iyabo, dakatar mata zanyi domin babu abinda zaku ji daga gareni. Dukkanninku kuna da matsayi na musamman a zuchiyata" Ajjiyar zuchiya ta sauke. Ranta yayi matuƙar ɓaci ainun, idanunta kuma sun rufe da kishi. Amman a zuchiyarta tasan ita ke da laifi da bata cakalo zancan ba da ba'ayi ba ma balle har ya tsayar mata. "Karshen watannan inaso zan leƙa Najeriya in dubo su Babala da yaran wajena in Allah ya nuna mana da rai da Lafiya." Cikin dakiya tace. "Allah ya nuna mana lokacin" Ya amsa mata da "Ameen" Shiru ya sake wanzuwa a tsakaninsu na kusan minti biyar cur, Gwadabe ne ya daure yace. "Kishi yau ya hanaki yin magana ko Hadiza? Bansan me yasa kike damun zuchiyarki har haka ba wallahi. Mata ku dinga sassautama rayukanku akan kishi ko a zauna lafiya " Kallonshi tayi ido a cikin ido tace. "Ashe kishin abinda kake so yana iya zama illa ni ban sani ba? Ai na ɗauka wanda yake da girman daraja ake kishi ba wanda bai isa ba" Kai ya dafe tare da lumshe idanunshi. "Yi haƙuri Hadiza kinji. Bance laifi bane dan kin nuna kishinki a gareni ba. Amman tunda lamarinnan ya faru baki bar zuchiyata ta zauna lafiya ba. Kinga na dawo a mugun gajiye yau. Hira dake yana warware dukkan gajiyar dana kwaso. Amman yau ke da kan ki kike shirin labto mun wata gajiyar ta daban ma" Yayi maganar da irin sigar daɗin bakin maza mai zurma matan da basu gane kan rijalu ba ( Ummu nabeeha ana magana) Jin ya faɗi haka ne yasa ta ɗan sassauto har suka taɓa hirar dai ba wani armashi. Haka kwanaki sukaita tafiya dare ya shigo, haske ya maye gurbinshi. Gwadabe sai ɗan siyan tsaraba yake yi yana adanawa kafin zuwan lokacin tafiyarshi. Baba Fhatsima itama sai shirin tafiya take ta tayi. Matan gidan kuwa sai tashin hankali ya ƙaru a garesu. Cikin kwana goma suka shirya tsab da yamma Tasi'u ya ɗaukesu izuwa Airport. Al'amarin daya mugun tada tarzoma mai girma a gidan bayan tafiyarsu Malam. Dan Baba Asshi tana kuka a tsakar gida ta dinga kiran iyayen Baba Fhatsima tana kunduma musu ashariya. Hakanne ya tunzura Hadiza da su Auwala da shigowarsu kenan. Al'amarin dai baiyi daɗi ba sam, Yaya Tasi'u ne ya dakatar da faɗan ta hanyar yin hargagi ga ƙannen nashi akan kowa ya kama gabanshi. Dan samarin ɗakin Baba Asshi ma sun shiga rikicin. "Ku yi haƙuri Baba. A dai dinga kai zuchiya nesa. Ya kamata ace yanzu maƙota sun dena jiyo sautin faɗa da ashariya daga gidan Malam. Wannan al'amarin tun muna yara aketa faman yinshi har yanzu tsugunne bata ƙareba. Ya kamata ace mun haɗe kawunanmu tun kafin wankin hula ya kaimu ga dare" Cewar Yaya Tasi'u kenan cikin takaici da baƙin cikin irin rarrabuwar kawunan dake cikin gidansu. Inama zasu yadda a haɗe a zama abu guda. Amman kash an bar kari tun ran tubani. Malam shi ke da sa sannu a faruwar komai, kuma yafi kowa da kowa son ganin ya haɗe kan ahalinshi sun dawo abun sha'awa a yanzu da yake ganin kamar wankin hula na shirin kaishi dare fa" BABA FHATSIMA A hotel ɗin dake bayan harami aka sauke Malaman da aka zaɓe aka biya ma aikin umara su da iyalinsu. A baya malam ya samu ire_iren kyautuka irin wannan, kujerar aikin Hajj ma da suka yi da Baba Fhatsima na farko wani ɗan siyasa ne Babba ya bashi, a sakamakon adda'a da malam yake taimaka mishi dashi, kuma yana ganin buɗin haka. Sun je umara da dama, gashi a wannan karon ma Allah ya nufa da'itan za'a sake komawa. Zaune take akan kujerar dake ɗakin hotel ɗin. Tana jiyo zubar ruwan wankan malam a ƙasa. Zuchiyarta sai take jinta fes Kamar babu wata damuwa dake ƙunshe a cikinta tsawon shekaru. Tunani ta faɗa mai zurfi. Tana tuno lokacin da suka sauka a wannan hotel da suke ciki a shekarun baya. A lokacin Malam yana ji da'ita yana girmamata fiye da tunanin me tunani. Bata mance wasu kalamai da malam ya faɗa mata a ranar da suka shigo makkah da daddare bayan sun gabatar da mu'amalar aure ba. "Fhatsima samunki nasarane babba a cikin rayuwata. Wallahi Fatsima jina nake yi tamkar wawa soko muddin bana tare dake. A duk lokacin dana kalli ƙwayar idanunki su kaɗai ka iya sauke mun dukkannin damuwata, duk girman matsalar da nake ciki. Ƴan siyasar da muke mu'amala dasu da dama sun sha bani ɗiyoyinsu in aura. Amman Fhatsima nasan ni naki ne ke kaɗai bazan iya haɗa soyayyarki da ko wacce mace ba a faɗin duniyarnan da muke ciki ba." Fitowar Malam ita ta katse mata zaren tunaninta ta dawo duniyar mutane. Ido malam ya zuba mata ƙur, jin kaifin idanunshi yasa ta ɗago kai suka haɗa idanu. Amman me sai malam yaga kwantaccen hawaye a guraben idanun Fhatsima. Zama yayi a kusa da'ita ya kama hannunta dukka biyu, ɗumin tafukan hannun juna ya ratsasu sosai. Ƙunshinta yake bi da kallo yanda aka jera salateb ( suffa,) akayi ado dashi cikin hikima, lallen ya sake fito da kyawu da hasken hannun nata. "Fhatsima wannan lallen nawa ne akayi mun?" Ya faɗa a mugun raunace dan ji yake kamar yayi kuka. Shi kaɗai yasan irin gasuwar da ruhinshi da gangar jikinshi take yi. Itama a sanyaye tace. "In ba kai ba Magaji wa zanyi ma lalle uban ƴaƴana?" A sanyaye cike da kunya yace da mamaki ya dubeta dan yasan in tana cikin yarda dashine har take iya kiranshi da Magaji a keɓe, amman dama a cikin mutane da cikin fishi Malam duk take kiranshi." "Fhatsima yau ni kika kira da uban ƴaƴanki, kuma kikace domina kikai wannan lallen?" Murmushi tayi tace. "Magaji ai har yau har gobe ruwa na maganin dauɗa" Farin cikine marar misaltuwa ya lulluɓeshi. "Fhatsima nayi kewar kasancewa tare dake, nayi kewar rashin samun cikakken lokaci kamar yadda kika sabarmun, nayi kewar kulawarki, nayi kewar tausasamun da kike yi Fhatsima. Na sani ni nayi kuskuren ruguza amincin dake tsakanina dake. Wanda in kin tambayeni dalili bani dashi wallahi. Nayi nadamar komai, ina takaicin faruwar komai Fhatsima. Hawayene tab a guraben idanunshi, yana ta girgiza kai irin na kaico. "Magaji cutuwa iya cutuwa nayi, tun daga lokacin da abubbuwa sukaita faffaruwa dauriyaa kawai nake yi, da ba a iya hawan jini abun zai tsaya ba, numfashina zai rabani dashi, in Barka a duniya da matan naka na so" Ɗan murmusawa yayi kawai. Baice komaiba ta ɗaura da cewar. "Na fuskanci wulaƙanci da matsi wanda ni kaina bansan ina da irin wannan haƙurin ba. Soyayyarka data yaranmu ce kaɗai tasa naci gaba da rayuwa da matanka. Burina shine ace da kaina naba ɗiyoyinmu tarbiyya a bisa doron alƙawarin da nayi maka tun kafin aurenmu. To Alhamdulillah na sauke nauyi" "Gashi ƴaƴan da suka fito a ɗakinki sun kasance sanyi da hasken idaniyata Fhatsima. Sun kasance abun alfahari kuma jagorori. Wannan kaɗai wata babbar nasarace a gareki, kuma hakan ya ƙara tabbatar dake a matsayin shugaba kuma uwar gida a gidan Magaji. Ko wacce mace da ƴaƴanta, dani kaina Magaji a cikin rigar alfarmarki nake Fhatsima " Idanu ta ƙura mishi tana mishi dariya shima dariyar yake yi. "Magaji kai da kaya mallakar wuya ne. Kuma ba'a hana ma ba da rago fata, tuwo baya canja sunanshi. Yarannan baka ragesu da komai ba tun yarintarsu har zuwa yanzu da nake wannan maganar. Fatana Allah ya haɗe kan iyalin naka baki ɗaya. Duk da kai da kan ka ka farraƙa haular gidanka, kasan....." "Ya isa Fhatsima kar ki rusamun farin cikin dake ƙunshe a raina" Ya katseta da hanzari. "Inaso ki tsaya mun kuma ki taimaka mun ke da Tasi'u da Jamila mu haɗu mu haɗa kan iyalinmu. Abinda ya wuce ya wuce, kece zaki taimaka komai ya gudana. Sannan haɗe yaran da matansu ni inata jaddadawa kamar zai iya gyara lamarin. In kan yaran ya haɗe, dole iyayen su shafa ma kansu ruwa. Asshi ce dai nasan zata ba da wahala. Ammam fa a shirye nake tsab da in rabu da duk matar da zata kawo mun taurin kai. So nake in gyara abinda na ɓata tun da rayuwata kar in bar baya da ƙura." Ajjiyar zuchiya Baba Fhatsima ta sauke. Yayin da take hasko abubbuwan da suka zama sune sababin faruwar waɗannan matsaltsalu na gidan Malam. Gani take yi kamar yanzu suke faruwa. "Baki ce uffan ba Fhatsima" Ya jefeta da tambayar. "Malam a ɗayan biyu ne wannan haɗe yaran da kai da Tasi'u kuke ganin zai yi tasiri wajen kawo soyayya da shaƙuwa a tsakankanin yaranka. Hakan zai iya faruwa, ko kuma hakan ya sake farraƙa kan yaran, ko da ta Hanyar matayensu, ko ƴaƴan da zasu hayayyafa. Malam wannan lamarin babbane. Amman mu dage da roƙon rabbil izzatu. Gamu a ƙasa mai tsarki mu dage da adda'a Allah yasa hakan ya zama matattakalar da zamu hau tsanin da zai wanzar da farin ciki a tsakanin Ahalinka. Sannan sai ka sanya dokoki masu tsanani, kayi ƙoƙarin dogewa akan dokokin. Kar ka faɗesu ba tare da ka basu mahimmanci ba, wannan raunin naka yana ɗaya daga cikin abinda ya soma kawo rarrabuwar kai a tsakankanin Ahalinka." A taƙaice dai sun jima sunata tattauna yanda za'a ɓullo ma lamarin. Sun yi adda'a sosai. Malam da Baba Fhatsima sun sasanta kansu sai ɓarzar Amarci ma suke yi abinsu. Sai yanzu ne Malam ya dawo cikin nutsuwa da hayyacinshi. Ya saki ajjihu wajen ganin ya kyautatama Baba Fhatsima, duk da ragowar mata da ƴaƴanshi ma bai barsu a baya ba. Gwadabe. Ana gobe Gwadabe zai kama hanyar Najeriya. Sun sha hira ainun da Hadiza da ƙyar ta barshi ya samu ya shiga ciki yaci gaba da shirya kayan tafiya. Kishine ɗamfare a ƙirjin Hadiza dan ita gabaki ɗaya a tunaninta Gwadabe baibai kawai ya ninketa amman wajen Shafa yake son zuwa. Shadda dalleliya da ƴan kunne Hadiza ta bayar a kaima Babala, ta bada agogo mai kyau tace ya kaima Shafa. Anty Badi'a kuma ta ba da takalmi da mayafi tace akaima Babala. Yaya Tasi'u kuma kuɗi ya bayar akai mata, sai ƙarin guziri da yaba Gwadabe. Sassafe kuwa Mammada ya rakashi tashar mota. Motarsu ta ɗaga zuwa Najeriya. A garin Kano ta dabo tumbin giwa Gwadabe ya sauka. Misalin ƙarfe tara na dare dake motarsu ta samu matsala a hanya sun daɗe a yashe a titi sosai. Sakkowarshi daga mota ita ta kara mishi damuwar rasa Iyabo da yayi a rayuwarshi. Gashi dare yayi, kuma bazai taɓa iya taka kafarshi zuwa gidan Yaya Hambali ba. Bashi da zaɓin daya wuce ya nemi gidan kwana a tasha, gobe sassafe yana son ya leƙa gidansu Iyabo ko Allah zai yi ko juna su gani, su gaisa kafin ya tafi. "Malam muna da ɗakin saukar baƙi in kana da buƙata. In kuma a Kano tafiyarka ta ƙare akwai tasi da Bus a bakin tasha zata kai ka duk inda kake buƙata. Cewar wani ɗan yuniyon. "Inada buƙatar ɗakin, Takai zan wuce zuwa gobe da safe dan Allah" "Nera hamsin kuɗin kwana, in bawali zaka yi a banɗaki kuma nera biyar, ba haya nera goma, wanka nera ashirin, ruwan zafi ma ashirin." Wani ɗan yuniyon dinne yace. "Haruna ka fiye surutu, ka ɗauki jakarshi dallah ka rakashi masauki" Wanda aka kira Haruna ya tuntsure da dariya yace. "Ai gara muyi gwari_gwari dai." Jakar kayan Gwadabe ya saɓa a bayanshi yace. "Biyoni muje in kai ka" A baya Gwadabe ya bishi zuwa can cikin tashar, wani gida mai kama dana masu zaman banza suka shiga. Maza da mata, da ƴan daudu ne a cakuɗe suna caca, masu ƙidan garaya kuma sai kiɗa suke yi, ga masu shan tabar sigari, ga masu cin goro da tomtom kowa dai da abinda yakeyi. Ƙyauran wani ɗaki Haruna ya buɗe suka shiga. Matasane a ciki fin su takwas, wasu sunyi bacci, wasu na bacci, wasu abinci suke ci. Tabarmace malala a ɗakin, sai kayi matashin kai da buhun kayanka. Gwadabe bai gama ƙarema dakin kallo ba Haruna ya miƙo mishi hannunshi. Nera hamsin ya bashi. "To ka raɓa ta can lungun ka kwanta. Kana buƙatar abinci ne?' "E ina buƙata, amman tuwo nake so" Haruna yace. "Tuwo miyar kukace kaɗai tayi ragowa. Ko wacce malmala nera ashirin ce, nama kuma ko wanne tsoka nera goma, man shanu ko wanne cokali nera biyar" Dariya Gwadabe yayi, duk da damuwar da yake ciki. Shima harunan dariya yayi. Nera ɗari ya miƙa mishi. "To a haɗa komai da komai na ɗari harda ruwan sha" Zaman Gwadabe ke da wuya sai ga kiran wayar Shafa. "Assalamu alaikum Shafa barka da dare, har izuwa irin wannan lokacin baki yi bacci ba?" Ɗan murmusawa tayi, cikin taushi da zaƙin murya tace. "Na kasa baccin inata jiran kiranka kace mun ka isa Takai in samu nutsuwar ruhi tukunna. Jin shiru ne yasa nace dai bari in nemeka" Ɗan murmushin wahala yayi mata yace. "Ayya. Kin ganni a Kano bamu daɗe da shigowa ba ma. Sai zuwa gobe in Allah ya kaimu zan karasa takai ɗin." Iska ta fesar daga bakinta. "To Allah ya nuna mana. Bari in barka ka samu ka huta, zuwa safiya in ka isa Takai mayi waya" Bai bata amsaba ƙit wayar ta ɗauke chaji ya ƙare, a ajjihu ya wurga wayar ya samu ya gyara zaman ƙatuwar jakar buhunshi. Wata budurwace ta shigo mishi da tuwo. Bayan ya gama ci kuma sai yayi jigum a zaune yanata faman tunanin yadda za'ayi gobe kafin tafiyarshi yaga Iyabo ko da basu yi magana ba. Wata zuchiyar tace dashi."ƙila ma tana can gidan mijinta ta mance dakai" take gabanshi ya tattake ya faɗi. Da wannan zulumin ya kwana. Sassafe bayan sallar asuba ya fice a tashar bayan yaba Haruna ajjiyar jakar kayanshi. Kai tsaye motar layin su Iyabo ya shiga. Tun daga hango gidan damuwarshi ta sake yin tsanani, bugun zuchiyarshi yaci gaba da ƙarfi. Iyaa Debisi ya hango tana ma yara masu kawo niƙa niƙan wani abu haka kamar gero, kamar dawa. Yana isa wajen ta kalleshi ta zuba mishi harara harda tsaƙi, ta mayar da hankali a kan niƙanta. Shi ko ƙiƙam yayi yana jiran ta kashe injin ɗin su gaisa. Amman bayan fa gaisuwar baisan me zai soma cewa ba. Ya NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BOOK 2 6 Yaya Hambali ya gano a zaune ya jingina da garu, Babala tana zaune a kujera, Auta na ƙasa a gefen ƙafar Babala. Ɗakin Babala yasha gyara kujerunma sababbi fil, hatta labule sababbi ne aka zuba. "Babala lafiya na ganku kunyi jigum? "Hmm lafiya ba lafiya ba Gwadabe. Kaine a tafe sassafe haka?" Babala ta bashi amsa. Waje ya samu ya zauna, Babala ya soma gaisarwa, kafin Yaya Hambali. Babu yabo babu fallasa ya amsa, dan ko juyowa ya kalleshi bai samu wannan darajar ba. Auta ce tace. "Yaya Gwadabe sannu da zuwa" Jiki a mace yace. "Yauwa Auta, ya mai gidan naki?" Shiru bata amsaba, Babala tace. "Yaya ka baro su Yaya Magaji, da fitinannun matanshi marasa daraja?" Ɗan murmushi yayi, a ranshi yace. "Babala ba zata canja ba" A fili kuma yace. "Malam yana Saudiyya shi da Baba Fhatsima yau kwanansu biyar ma. Duk kowa yana lafiya, sunce ma in gaisheki" Mikewa tsulum Yaya Hambali yayi. "Babala ki gama dashi na dawo in kum gama. Dan bazan iya zama inuwa ɗaya da wannan kangararren yaron marar jin maganarki ba" Yana gama faɗin haka ya fice, Gwadabe ya bishi da idanu galala. Babala ta amsa mishi da cewa. "Kangararre fa, yaro aita nuna mishi annabi yana runtse idanu. Ni kaga banyi ma tunanin zai sake zuwa dubamu ba" Yaya Hambali dake tsaye yana sa takalmi yace. "Sabida Bara'u ƙanin ubanshi yazo, da wannan ɗan nashi me cakuɗe da jinin yarbawa ai" Yana gama kunna Babala yayi tafiyarshi. Ai fa nan Babala ta inda take shiga ba tanan take fita ba. "Shima Bara'un ashe kangararrene irinka?. Yasa wannan yaro ɗan wajen beyerabiyar tsohuwar matarka a makarantar boko Har gida naje na samu Sakina matarshi nace da'ita ina son ganin shi Bara'un. Wallahi ko da yazo na zayyanama Bara'u bana son wannnan ɗa yayi boko. Yaronnan ya shafa toka a idanunshi yace in yi haƙuri dole a yanzu yara suna buƙatar ilimin boko. Ko da wanku ya shiga zancan ƙarshe ma Bara'u ce mai yayi ai shima yaranshi na zuwa boko dole shima wannan ɗan yarbawa yayi boko. Zan yi maganinku dukka, har wajen uwarshi naje na kai ƙararshi ai" Gwadabe dai yayi jim yana saurarenta sai zuga faɗa take yi. Sai da ta gama tayi mai isarta yace. "Ayi haƙuri dai Babala dan Allah." Hannu yasa a ajjihu ya zaro kuɗin da Yaya Tasi'u ya bashi ya kawo mata." "Ga wannan inji Yaya Tasi'u yace a kawo miki, matarshi ma ta bada tsaraba" Hannu tasa ta fisge kuɗin da ƙarfi. Gwadabe dai in da sabo ya saba. Tsarabar daya tawo dashi duk ya cicciro ya baza a gaban Babala. Yadinga mata bayanin mutanen gida da za a rarrabama. Ya ware nata dana Auta dana Yaya Halima. "Banga na yayyenka su Fodiyo ba, balle nasu Da u. Me kake nufi kenan Gwadabe?" Sauke kai yayi ƙasa yayi jim kaɗan. "Kiyi haƙuri nan gaba in zan tawo zan tawo musu dashi, amman yanzu kam babu nasu" "Baka isaba dan ubanka. Yayanku meye a rayuwarnan bai yi maka ba? Ya ciyar dakai ya shayar dakai, yayi maka sutura, ya goyaka a bayanshi ya kai ka makarantar allo data boko da guminshi. Yau sabida wata ƴar iskar beyerabiya shine kake shirin yanke halaƙarka da ƴan uwanka maza? To ni zan tattare duk abinda ka bani in basu bana buƙatar ka sake kawo mun komai madamar ba zaka baiwa ƴan uwanka ba. Kasan ai sunfi ƙarfinka ta ɓangaren arziki. Yanzu haka duk mota suke ja har Da'u. Jebeka kai a fige a bushe, sai uban naɗin buzaye a ƙaron kanka. In baka yi wasa ba ma a haka zaka ƙare Gwadabe" hawayene suka gangaro da gudu zuwa kan kuncinshi. Ya kasa furta daidai da kalma. "Bama son duk abinda zai fito daga hannunka Gwadabe. Munfi ƙarfinka,tun da majina a hancinka nake juya kuɗi. Da wasa kar kayi gigi ƙafarka ta tako gidana bana son yin hulɗa da kai har gaban abada mitsiyaci" Cewar Yaya Hambali dake tsaye a dokin ƙofa, yaji dukkan tattaunawar Gwadabe da Babala kan tsaraba. Babala ta turo ma Gwadabe tsarabar da yayo mata dana su Yaya Halima. "Gashi dani da ƴaƴana bama buƙatar komai daga gareka. Wannan dai da aka baka saƙo ka kawo mun na karɓa. Matan gida kuma kaje ka rarraba musu da kan ka" "Babala kiy mun rai kiyi haƙuri. Yaya Hambali kaima kayi haƙuri. Duk tsawon watanninnan tsarabarnan nake ta siye ina jefarwa. Iyakar abinda kuɗina ya iya siya kenan." Ya faɗa cikin sigar rarrashi. Kamar sake tunzura Yaya Hambali yayi ma. "Shine nace maka kaine mitsiyaci Gwadabe. Dan wannan duk tsarabar bata wuce in siyeta a take in bayar da'ita sadaka ba" Babala tace. "Faɗa mishi dai. Baka ga yanda arzikinshi yaci uban nada bane. Gidanshi na kano an ruguje ya dawo gidan bene Ai kaga yanda gidannam ya dawo ko gidan mai gari albarka, ga babbar motarshi a ƙofar gida" Gwadabe yana zaune suka ƙare mishi tanadi tsab, ko tari baiyi ba, idanunshi sun kaɗa sun zama jawur. Yanzu iyayenmu sun zama abinda suka zama. Nuna fifiko akan ƴaƴansu masu sukuni akan waɗanda su Allah bai basu ba. Miƙewa yayi da tsarabar matan gidan ya kaima Goggo Yabi yace ta raba a tsakankaninsu. Bayan ya dawo ɗakin Babala ne tace. "Ya batun Aure, ko kanaso kace ba zaka sake aure bane tunda ka rabu da ƙanwar uwarka Iyatu? Ga Laila tayi aurenta, yarinya da kyanta Allah ya taimaketa ta auri mashahurin ɗan siyasa, baka ga gidanta ba." "Aure zanyi Babala. Baba Magaji ya haɗani da ƴarshi Bazawara Hadiza harma mun sasanta kanmu, Lokaci kawai ake jira. Kuma..." Ta katseshi da cewa. "Kuma me? Dama shi Yaya Magaji abinda yake so kenan shi yasa ya goyi bayanka ka bijere akan auren Laila, ashe tashi ƴar yake ma tanadin talaka kamarka? Na lura so yake ya yanke zumunci damu, domin matsawar Iyatu taji wannan batu zata yi fishi. Dan kawai Allah ya jarabceta da ɗiya me ciwon sata." Nan Babala taita jujjuya zancan. Gwadabe na son ya faɗa mata batun ƙanwar Tamu, amman tsoro ya hanashi, dole ya ja bakinshi ya tsuke. "Babala ni zan shiga ciki in yi wanka. Jazuli yana ciki ne?" Ya tambaya da dariya a ƙoƙarinshi na danne damuwar data addabi zuchiyarshi. "Ka dai je ɗakin nasan a buɗe yake. Wake zama baya neman arziki? Jazuli yana Kano Yayanku ya buɗe mishi shago, ya kan dai shigo Takai lokaci zuwa lokaci" Kai kawai ya girgiza ya ɗauki jakarshi yana shirin fita Babala tace. "Kazo ka kwashi tsiyarka fa Gwadabe" Fita yayi tare da cewa. "Ni lada nake nema. Ko zubarwa kikayi daidai ne Babala" Har yabar barayin bai dena juyo sababin Babala ba. Wanka yayi ya shiga ɗakin Jazuli ya zauna a bakin katifa yana mai cike da zulumin irin furucin da Babala ta daɗe tana jifanshi dashi na rashin arziki. Gashi duk abinda yasa a gaba baya samun nasara sam. Ko haƙon zinari ya shiga rijiyar zaiyi. To sai dai fa yasha wahalar banza. Sau huɗu ya taɓa samun dutsen zinare ƙananu suma. Amman Auwala da Mammada sau nawa suka samu, sai dai fa in an siyar su ɗan tsakura mishi na kashewa. Dan aikin haƙan zinare ba aiki bane na wasa, balle har wanda ya haƙa ya baka kuɗi me yawa, aikine mai cinye ƙarfi da ƙuruciya sosai. A hakanma yaga ƙoƙarin su Auwala da suke sammishi wani abun. Dan kullum fa a cikin shan ƙwayar bature suke maganin ciyon gabɓai. Ga auren mata biyu a gabanshi, bai tara ba bai ba wani ajjiya ba. Atampa biyu kawai ya ajjiye. Auwala kuwa ya gama haɗa kayan akwatinshi tsab, takalmane kawai ya rage. Iska ya furzar a bakinshi a fili yace. "Anya bazan fito in faɗa ma Tamu gaskiya ba kuwa? Ni bani da ƙarfi, kar in auri mata biyu in zo in gaza wajen kulawa dasu. Yana da kyau Tamu yasan yanayin samuna fa. Amman bari inje in samu Bara'u inji ta bakinshi" Zuruf ya miƙe cikinshi ya wani juya mishi. Sai lokacin ya tuna ashe fa baici abinci ba ma. A ƙofar gida ya tarad da Yaya Hambali da abokinshi Inusa yaron mai gari. "Gwadabe kaine a garin namu?" Ya tambeshi da fara'a. Fuska Gwadabe ya sake ya miƙa ma Inusa hannu suka gaisa. "Ciwo kayi ne Gwadabe, kai kaga yanda duk ka faɗa kuwa?" Kai Gwadabe ya sosa kana yace. "Sha'anin rayuwa ce kawai Yaya Inusa. Yau da gobe bata bar komai ba, a dai samu a adda'a" Girgiza kai yayi cikin tausayawa yace. "Allah ya rufa asiri. Zamu yi magana da Hambali muga me ya dace a taimaka maka dashi" Buɗar bakin Yaya Hambali yace. "Da za a taimaka mishi da bama zaka ganshi a haka ba. A lokacin da naso in taimaka mishi ai ƙi yayi. Inusa in dai kanaso zumuncinmu yaci gaba, to kar ka sake ka taimaki Gwadabe da sisin kwabo" Sai wani huci yake yi, yana hura hanci. Yaci jar shadda dinkin tazarce, idanunshi cike dam da farin kwalli. Murmushi Gwadabe yayi kawai ya wucesu. Tafiya kawai yake yi, amman baya ma iya ganin gabanshi. Tunanin shi kuwa shine. Anya Babala itace ta tsugunna ta haifeshi kuwa? Anya su Yaya Hambali ƴan uwanshi ne su kuwa? Sai dai yana tuna yanda suka taso cike da kulawar Yaya Hambali, ya kuma haɗe kawunansu duka, cikin soyayya yake musu komai. Har wanka yayi musu da hannunshi. Gashi da yawan taimako, hakannema yasa gashi duk ya jaye ƴan uwan nashi, kuma dukkansu da bazarshi suke taka rawa. Daga sanda ya Auri Iyabo zuwa yanzu yana ganin ƙiyayya. Sun kwana basu ci abinci ba, yaje wajen ƴan uwanshi ya bisu kab aka rasa wanda zai taimaka musu. Hawayene yaji suna zuba a idanunshi shaa. Da sauri ya goge yana dariya kamar mahaukaci. Ko da yayi salllama a gidan Bara'u, Sakina ce ta fito. Tayi mamakin ganin irin ramar da Gwadabe yayi. Bayan sun gaisa ne take cewa. "Gashi yana gona. Amman bari insa Shehu yayo kiranshi. Ka shigo daga tsakar gida" "Nagode Sakina" A sanyaye ya shiga tsakar gidan. Ya zauna akan taburmar daya samu a shimfiɗe a baranda yayi saroro dashi. Ruwa Sakina ta kawo mishi, sai da yasha sannan yace. "Ina yaran ke kaɗaice a gidan?" "Sun tafi makarantar allo dake yau babu boko. Ƴan kuci_kucin kuma Baban ya tafi dasu gona. Ya wajen su Baba Magaji?" Ɗan murmusawa yayi kafin yace. "Kowa yana lafiya, sannu fa da ɗawainiya Sakina allahu ya bar zumunci" Dariya tayi ta miƙe abinti taci gaba da kaye_kayenta har Bara'u yayo sallama ya shigo. Ganin Gwadabe ne yasa yayi Dariya, sai dai ya girgiza da yanayin daya ganshi a ciki, musamman baƙi da ramar da yayi. Ga wani rawani daya tuntuma a kanshi irin na buzaye. "Baƙin buzu gallah mu ka yi a gidan namu, Gwadabe maraba lale" Zama yayi suka tafa. Sakina ta dure musu ɗumemen dambu yaji rama da man shanu. "Fara cin abinci tukunna mu sha labari" Sai da Gwadabe ya ƙoshi ya sha ruwa kana yace. "Na sameku Lafiya ya ɗawainiya?" "Lafiya lau, ɗawainiya ai yiwa kaine Gwadabe. Ya bayan rabuwa?" Ɗan sauke kai ƙasa yayi yana wasa da yatsun ƙafarshi yace. "Sai alkhairi Bara'u. Ya gona?" Dariya yayi yace. "Gona lafiya lau, sai godiyar Allah. Lafiya irin wannan ramar haka Gwadabe, ciwo kayi mu bamu sani ba ko me?" Bara'u ya faɗa cikin kulawa. Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke kana yace. "Wallahi babu ciwo yau ce kawai Bara'u. Ga ciwon damuwar rabuwa da iyali lokaci guda shima yana damuna ainun. Kuma sana'ar tamu tana da wahalar gaske" Ajjiyar zuchiya Bara'u shima yayi. "Toh Allah ya kawo maka mafita. Ai rashin iyali ga wanda yasan daɗinsu babban tashin hankali ne. Sannan ya haɗema har da yanayin can ƙasar kasan baka sababa. Amman ya batun aurenka da Shafa da Hadiza?" "To Bara'u ni fa gani nake yi in haƙura da Shafa kawai. Bana jin motsin san su sam a raina. Ganin girman waɗanda suka mun kyautarsu kawai nake ji. Ka ganni sai in yi sati biyu ban riƙe nera biyar tawa ba. Da haka ne zan auri mata biyu? Atampa biyu kawai na iya ajjiyewa da sunan kayan akwati fa. Duk da Tamu zai taimaka mun, amman dole inma Hadiza" Shiru Bara'u yayi yana nazarin maganar Gwadabe, domin maganarshi abun dubawace. "To Gwadabe maganarka gaskiya ce domin Allah. Amman dole a nemi maslaha, kasan Tamu ba lallai yaji daɗi ba. Shafa kuma ta gama sa ranta da kai. A gidansu duk ansan da maganar aurenku fa. Ni ina ganin ka daure dai ka auresu du biyun. Sai a tura bikin ita Shafa zuwa nan da ko shekara ne. In yaso ita Hadizan sai ka soma aurenta. Ko yaya kake gani?" Kai Gwadabe ya gyaɗa kafin yace. "To hakanma gaskiya ne. Nima abinda du ya dameni kenan. Kaga kuwa in da za a ɗaga ɗin zuwa lokacin da ka ambata ɗin da abun zaiyi kyau. Muna sa rai abubbuwa zasu warware da izinin Allah. Dan sana'ar tamu in Allah ya dafa ma mutum yana samun arziki. Da ace ina da wasu jari ma a hannuna da abun sana'a zan dinga tafiya dashi ina ɗan siyarwa haka. A samu ɗan na kashewa." Bara'u yace . "Ga shawara kana ganin in kana siyar da magungunan gargajiya ba zaka samu ciniki ba? Da sai ka jaraba ai, ko maganin dattin ciki, da maganin basir, da ɗan na warware gaɓoɓi da sai ka dinga dafawa kana ƙullawa a leda kana tafiya dashi. Kuma fa akwai riba." Shiru Gwadabe yayi yana nazari kafin yace. "Wannan ma shawarace Bara'u. Sai in jarraba, in zan tafi zan tafi da wasu saƙe saƙin in sha Allah" "Sai kaga Yaya Hambali ya gyare gida ko?" Yayi maganar yana dariya" Gwadabe yace. "Gida yayi kyau sosai Bara'u, sai haska gari yake yi." "Hmmm ai Yaya Hambali in faɗa maka harkace ta buɗe mishi. Wani bawan Allah ne ya bashi kwangilar dabino, da jar dawa ko buhu nawa yakai yana siya. Kai duk inda dabino da jar dawa suke Yaya Hambali siye su yake yi ya kaima mutuminnan. Shi yasa bashi da aiki sai zuwa ƙauyuka ƙauyuka neman jar dawa Ance gidanshi na kano ya rushe ya maisheshi bene. Kuma ya sai gonakai shimfiɗa_shimfiɗa a bayan gidan gonar mai gari baka ga girmansu ba, wai yanaso bana yayi noman jar dawa ne." Gwadabe ya taya ɗan uwan nashi murna sosai. Har cikin ranshi yaji farin ciki, yasan ko babu komai Babala zata huta. "Ni na mance sai kazo kaga Auta a gida miji ya sakota uwar miji ta hanata zaman lafiya " Cikin mamaki Gwadabe yace. "Autan aka saka Bara'u?" Baki Bara'u ya saki yace. "Wai baka ganta a gidan ba, ko dai baka tsaya kayi hira da Babala bane?" "Hmmm Bara'u kenan" Nan ya kwashe duk irin cin kashin da Babala da Yaya Hambali su ka yi mishi. Ya ɗaura da cewa. "Zuchiyata dab take da bugawa. Dame zanji Bara'u . Batun mutuwar auren Auta kuma duk Babala ce ta sa aka sakota, ta hanani zama da Iyabo, gashi uwar miji ta hana Auta zaman aure. Lokuta da dama iyayenmu suna kusa kurai" Tsit Bara'u yayi, idanunshi suka rine da kyar yace. "Hakane Gwadabe kayi haƙuri. Ni kaina Yaya Hambali babu irin cin mutuncin da bai yi mini ba akan sai dai in cire Toye daga boko. Dana faɗa mishi gaskiya kuma yace na zageshi. Gwadabe Babala har gidanmu taje ta kai ƙarana" Sun jima sosai suna tattaunawa. Da rana saiga ƴan makaranta. Toye ya girma abinshi, bai mance da mahaifinshi ba. Har iyabo Toye saida ya tambayi Gwadabe. Zuchiyar Gwadabe sai tayi sanyi jin yaron bai mance shi ba. Sai da daddare Gwadabe ya samu damar yin waya da Hadiza da Shafa.Kwanan Gwadabe biyu a Takai, amman zaman duk ya gundureshi sabida irin hantara da munanan furucin Babala a kanshi. Bayan ya huta sai kuma yabi dangi da gaisuwa gida_gida. Kwananshi Takwas yayi sallama dasu. Dashi da Bara'u suka dunguma Habuja wajen Tamu domin su yi mishi bayani akan batun ɗaga biki. Bayan sunci abinci sun huta. Ya ga ƴan biyu ya basu ƴar tsarabar da yayo musu da yaran Tamu, ganin yanda yaranshi su kai kyau da gani ana kulawa dasu, dan kayan jikinsu ma mai tsada ne. Raɗa yaima Bara'u a kunne yace "Maganar ɗaga bikinnan a barta Bara'u. Kunya duk ta lulluɓeni wallahi, jibi hidimar da yaketa yi da yara fa" Kai Bara'u ya gyaɗa halamar hakane. Fitowar Shafa itace ta dakatar da Tamu da magana dan tambayarsu yake yi gulmar me suke yi. Jus ta dire musu tasha ado tayi kyau tana ta ƙamshin turare me daɗi. Kanta a ƙasa ta gaishesu. Bara'u yace. "Ja ira yau mu ake jin kunya Shafa? Lallai kin girma" Murmushi kawai tayi mishi. Gwadabe sai kallonta yake yi yana murmushi. Tamu ne ya miƙe tsaye tare da cewa.." "Kafin su gama Bara'u tawo mu shiga kaga gari. Ai kwana zaku yi dai ko? Dan nasa Shafa ta gyara muku shago an sa katifa ma" Bara'u ya miƙe tsaye yace. "Kwana zamu yi kai bama ɗaya ba, dan wallahi ni kam saina huta. Kai kaji falonnan wani sanyin fanka kuwa?' Tafawa su kayi tare da ficewa. Fitarsu ce yasa hankalin Gwadabe dawowa gareta, itama saita gyara zamanta. Idanu ya ƙura mata ita kuma sai sinne kanta take yi kunya ta isheta. Shi kuma yau ne ya samu damar kallonta tsab. Yarinyace gaskiya, tana da madaidaicin kyau, da matsakaicin tsayi, bata da diri a kallon da yayi mata a tsaye, amman ƙirjinta a cike yake masha Allah. "Gani a gabanki amman kin kasa cewa dani komai. Ke da kika ce kinata mafarkin zuwan wannan ranar. Sai naga kin kasa cewa komai " Sake sunne kanta tayi ƙasa. Yawan kunyarta sai ya zama silar burgeshi, kunya tana yima ɗiya mace kyau, tana zama wani ado na musamman gareta. Murmushi yayi kawai tare da girgiza kai. Shafa tayi mishi ƙarama sosai shi yama rasa taya zasu yi wannan zance. Da dai taga shirun yayi yawa sai yace. "To a ɗago fuskar mana in ɗan kalla" Ɗagowa tayi ta ɗan kalleshi, shima ya kalleta, tayi saurin kawar da kanta tare da cewa. "Barka da isowa, ya ka baro mutanen Takai?" Sai da ya yi Dariya sosai kana yace. "Suna lafiya, ya karatu ya aikin kuma duk anayi ko?" "Anayi Alhamdulillah" "To Allah yayi jagora. Sannu da ɗawainiya da ƴan biyu. Ayashe ta sanar dani irin hidimar da kike yi dasu. Tamu kuma ya bani labarin irin shaƙuwar dake a tsakaninku. Kina son zaki tafi dasu ne in mu ka yi aure?" Ƙasa tayi da kanta tana wasa da yatsunta tace. "E inaso in tafi dasu, sabida zasu yi maraicina, kuma nima zanyi kewarsu da yawa. Gashi ba ƙasa ɗaya ba balle ince zan dinga sawa a kawo mana su hutu. To Amman Yaya Tamu yace babu wanda zai rabashi da su" Dariya Gwadabe yayi. Dariyar yadda take magana muryarta na rawa kamar tana gaban dodo." "Zan mishi magana in lokacin yayi. Dan inason in haɗe kan yarana. Toye dake wajen Bara'u ma zan ɗaukeshi in yaso sai in ba yayarki tayi riƙonshi. Zanfi samun nutsuwa" Da sauri ta ɗago tace. "Wacece Yayata kuma?" Kallonta yayi yana nazarinta, a muryarta yaji kishi. Sai ya basar yace. "Hadiza nake nufi ƴar uwata wacce zan haɗaku" A sanyaye tace. "Ka yanke hukuncin soma aurenta kafin ni kenan? Bayan ni aka soma baka kafin ita" jin furucinta da rawar muryarta sai yasa yaji kunya. Ba shiri yace. "Ko ɗaya Allah shine masanin wacece zata zama fari, in Allah yaso sai kiga rana ɗaya an ɗaura auren. Nace yayarki ne sabida Hadiza ta girmeki sosai. Bazawarace yaranta biyu" Ɗan boyayyen ajjiyar zuchiya ta sauke. A haka hirar taci gaba da gudana. Tsarabarta ya miƙa mata, ya miƙo mata agogon da Hadiza ta bayar a kawo mata. Har a fuskarta taji daɗin kyautar Hadiza sosai. Miƙewa Gwadabe yayi tsaye yace da'ita zashi masallaci an soma kiran sallar la'asar. Haka dai Gwadabe suka kwana biyu a gidan Tamu. Sunga karramawa sosai. Ranar juma'a ya kama hanyar nijer, Bara'u kuma ya kama hanyar Takai. IYABO. Tsarki ya tabbata ga Allah mai kowa mai komai. Sarkin dake da iko a kan kowa da komai. Muna zazzaune mata da maza sai shigowa suke ta faman yi. Fuskokin al'ummar cikin wannan jirgi mafiya yawansu cike take da annuri. Barinma ire_irenmu da bamu taɓa tunanin samun irin wannan damar ba ko a mafarki. Wata na'urace muka ciyo tana magana da turanci akan kowa ya ɗaura belt ɗinshi ya gyara zama zuwa minti sha biyar jirgi zai tashi. Ma'aikatan dake cikin jirgin sun taimaka mana ainun. Dan daga ni har Uwani bamu iya saka wannan bel na jikin kujera ba. Mintunan da wannan na'ura na cika jirgi ya soma tafiya da tayoyinshi a cikin filin girji. A hankali _a hankali har jirgi ya tashi sama. Sai da ya tsayu a sama kana na dawo cikin hayyacina dan juwa naji inaji harda hararwa. Wasu tsofaffi ma harda ihu dan tsoro. Taga na kalla na ganni a cikin gajimare. Gurun da Yaya Hamma ya bani na sake matsewa a hannuna na lumshe idanuna, abubbuwa ne suka haɗemun. Murna da kuma alhinin barin Dada. Da kuma damuwa da fargabar rashin furta mun kalmar soyayya da Yaya Hamma bai yi ba. Ta wani ɓangaren gani nake yi na rasa shima, musamman inna tuno da irin soyayyar da Daso take gwada mai. Bani da masaniyar sanda zuchiyata ta kamu da soyayyar Yaya Hamma. Ada nayi tunanin damuwa da lamarina shi ya haifarma da zuchiyata shaƙuwa dashi. Ayau rabuwarmu na sake samun yaƙinin motsin sone a ƙirjina bana shaƙuwa ba. Kuma a yaune na tabbatar da soyayyar da Yaya Hamma ya ke yi mini. Iska na furzar daga bakina. Idanu na sake lumshewa. Allah sarki Gwadabe yanzu inaji ina gani ni Iyabo na rasaka, dole in yi aure in hayayyafa da wani ɗa namiji bayanka. Ji nayi Uwani ta balbalin ta dafani. Juyowa nayi na dubeta, murmushi tayi mun, nima shi na mayar mata. "Iyabo, ko Hamma bai faɗa ba tsananin sonki yake yi sosai. Ki duba har kwalla sai da ya zubar, banda irin ɗawainiya da kulawar da yaita baki. Ya kamata ki kwantar da hankalinki dan nasan zuchiyarki bata iya kamuwa da soyayya ba. Sannan ki bari ki samu nutsuwa kiyi tunani akan wannan soyayyar. Ki sani dai Hamma a ruga yake rayuwa ba'a birni ba, nifa banga dalilin ma da zaki yi sake har zuchiyarki ta kamu da sonshi ba kema. Na fa yaba ma ƙoƙarinshi gaya, amman baima dace batun wani so ko aure ya ɓullo ba" Mrs Bukhari *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BOOK 2 7 Ajjiyar zuchiya na sauke. Uwani duk abinda kika faɗa gaskiya ne akan Yaya Hamma. Amman a jikina gani nake yi tunda bai furta mun kalmar soyayya ba har mu kai bankwana, to bazai furta mun ba. Kar ki manta kasarfa zamu bari, tunda muka shigo garin Kano ya dace ya fallasamun asirin zuchiyarshi ko?" Dariya Uwani tayi mun. "Iyabo manya. Maganarki haka take. Amman in kin lura Hamma baƙauyene cikakke, babu wayewa a tattare dashi. Ni nafi tunanin ya rasa ta yanda zai furta miki kalmar so ne. Amman a shawarce kar ki bari zuchiyarki tayi zurfi a soyayyar Hamma. Kar mu dawo kiga saɓanin abinda kike tunani azo a samu matsala. Shekara uku ba kwana uku bane. Kuma ƙila mu wuce tsawon wannan shekarun." Haka mu kaita tattauna zantuka ni da Uwani. Dare ya ratsa sararin samaniya sosai. Ma'aikatan cikin jirginne suka soma rabon ruwa da lemo, da soyayyen cincin, da naman kaza. Sai shillawa muke cikin gajimare. Awannmu 6 da minti ashirin muka ji jirginmu ya sauka. Dukkanmu muka cika da murna a tunaninmu mun iso Makka ne ashe ba haka bane, itofiya muka iso. Hajiya Salamatu ta sanar damu zamu kwana a Airport zuwa gobe jirginmu da zai ƙarasa damu saudiyya zai zo. Ta ɗaura da cewa. "Ni daga nan shine iyakata daku. In kuka sauka a Makka Hajiya Mangala zata turo duk a ɗauke ku. Allah ya ba da sa'ar abinda aka fito nema." Daga nan muka ɗunguma inda zamu kwana. Anan muka rarrama sallolin da ake binmu a filin Allah. Washe gari duku_duku jirgin da zai mayar da Hajiya Salamatu zuwa Najeriya ya tashi dasu, cike da fasinjojin Najeriya. Mu kuwa a gantale ga baƙar yinwa haka mu kai ta zama a wannan fili. Gashi cikinmu babu wacce take da kuɗi, ruwa ma sai da mu ka roƙa aka bamu, shima wasu basu samu ba. Sai kusan magriba aka sanar mana jirginmu yazo. A madadin Makka, sai akace ai dama Riyahd za'a kaimu. Haka aka ɗuramu a jirgi. Daga itofiya zuwa Riyahd Awa 2 da minti hamsin da huɗu ne ya kaimu. Aka sauke mu a filin jirgin. King khalid international airport. Tun daga sakkowarmu jikina ya mutu. Bani kaɗaiba duk tawagarmu jikinsu duk a mugun mace. Bayan mun je ɗakin ɗaukar jaka, daga nan aka nuna mana ƙofar fita, duk muka fito yu. Titine shimfiɗaɗɗe, sai tsirarin motoci masu shige da fice jefi, jefi. Ga wutacen lantarki masu haske kamar rana. Dan ko allurarkace ta faɗi zaka ganta kamar ba dare ba. Wata farar Hajiya ce ta nufomu tana murmushi, tasha gwala_gwalai haƙorin makka har guda shidda ne reras a bakinta. Da isowarta sai muka ji tayi Hausa raɗau. "Kune mutanen Hajiya Salamatu kano to jidda?" Kusan dukkanmu muka haɗa bakin wajen amsa mata da. "E mune Hajiya" Dariya tayi tace. "Masha Allah komai yayi kalas. Yalla ga mota bus ku shiga muje" mota muka shisshiga kowa ya zauna, iyakar galabaita dai munyi. Yinwa kuwa ba a maganarta. "Uwani nifa jikina ya mutu tunda akace Riyahd za a kawo mu. Domin ba haka mu ka yi da Hajiya Salamatu ba." Buɗar bakin Uwani tace. "Karma kiji komai Iyabo da Makka da Riyahd duk abu ɗaya ne. Kuma ƙila tana nufin a makka za a sama mana aikin wanke_wanken tunda mu ba zama mu ka zo yi ba." Sai data faɗi haka sai na ɗanji sanyi. Duk da dai zuchiyata a cike take da tsoro ainun. Tafiya kuwa tun anayin ta marmari, har abun yazo ya gunduremu, tun cikin dare muke sharara gudu bamu muka isa inda zamu je ba sai da asuba. A ƙofar wani babban gidan bene motarmu ta tsaya. Muka sassauko kowa a wahale, wasu tsofaffi daga cikinmu sai taimaka musu muka yi suka fito tsabar jigata duk sunyi fitsari a jiki. Hajiya Mangala ce ta fito daga cikin motar ta ta nufomu. "Yalla muje ciki, kun sha hanya, a yi wanka a karya sai kowacce ta kwanta ta huta kuma" A baya muka bita zuwa cikin gidannan. Ko wacce na faman tiri_tiri da kaya. Ni da Uwani ne kaɗai bamu da wasu wadatattun kaya, a jaka ɗaya ma muka haɗe kayan. A bene na shida muka tsaya. Mu dai duk inda Hajiya Mangala ta ɗaga ƙafarta anan muke sa tamu ƙafar. Wasu ɗakuna ne a jejjere reras a wani dogon falo, ko wacce ƙofa da number a jiki. Ɗaki na ashirin daga nan ta soma. "Mutum goma goma zaku shisshiga, daga wannan ɗakin zuwa har inda zai isheku. Amman wannan me lamba ashirin ɗin mutum biyu ake bukata. Ke da ke ku shiga nan tunda kune a tsaye a wajen." Ta nuna ni ni da Uwani muna tsaye riƙe gam da hannun juna. "Amman kafinnan ko wacce ta bani fasfo ɗinta da wayar salula in tana dashi. Ko wanne ɗaki akwai land line da zaku kira ƴan uwanku na Najeriya." Nan Uwani ta zaro wayarta ta miƙa, muka haɗe fasfo muka bata, na sanar mata bani da waya. Duk da haka sai da tasa wata mace ta caje kayanmu, ta caje jikinmu, hannunta har cikin wando, har ƙasan mama sai da ta ɗaga, da gashin kai. Tana gamawa damu muka shige wannan ɗaki da sallamarmu. Wallahi Allah sai da gabana ya yanke ya faɗi. Siririn gaske ne ɗakin, iyakar tsayin katifa, babu masaka tsinke. Ga mata nan su takwas a kwance ko wacce a karamar katifa irinta ƴan makaranta. Ragowar katifu biyun kuma jakunkuna ne akai a jibge. Daga bakin ƙofarnan da yake da ɗan sararin da muke tsaye, babu inda zamu ɗaga ƙafarmu mu ajjiyeta sai dai a katifar mutane. "Uwani na shiga uku, kinga wani ɗaki kamar kwanciyar kabari. Kafin uwani tayi magana aka buɗe ɗakin. Wannan matar data caje mu ce. "Dama nasan za'a rina wai an saci zanin mahaukaciya. Ke Ƴar ɗas, ƴar ɗas kina jina fa" Wacce aka kira da ƴar ɗas ta tashi zaune tana miƙa. Ni dai in ba gizo idanuna yake yi mini ba sai naga kamar namiji, akwai dai gashi a kanshi, amma ƙirjinshi babu komai a shafe, duk da akwai ƙunƙumar macce wacce bata da nono, kuma macece, inta haifu sai kan nono ya bulloƙo ta shayar da jaririn, to ina tunanin ko Ƴar Ɗas ƙunƙumace. "Oh ma'aikin Allah na Madina ni Ƴar Ɗas. Yanzu Taraliya duk illahirin jama'ar dake ɗakinnan saini kika ga damar tasa, sabida riƙaƙƙem iskanci? To gani gani" Magana take yi da lanƙwasa, gata da yanga" Wacce ta kira da Taraliya tace. "Baƙi mu ka samu, kisa waɗancan matan su kwashe kayansu a kafinsu, zasu kwanta su huta" Ƴar Ɗas tai mana kallon uku saura kwata tace. "Bayin Allah maraba da zuwa. Ke waccan tsalllako ga katifa can. Kiyi watsin ruwan tsarki da kayan da kika gani a katifar. Ke kuma ga bayan gidaa bayanki, faɗa ki shilla wanka, inba haka ba zafi ne zai kasheku" Dariya Taraliya ta saka tace. "Baki da dama yar Ɗas" Itama dariyar tayi tace. "To ai gani suke daɗi muke ji in mun baro gida Najeriya. Tunda sun shigo sai du a haɗu aci wuyar tare ai. Duk wacce ta kwace ta tafi Najeriya ta ba da labari" Take naji wani zum_zum. Tsoro ya kuma shigata. Ina tsaye Uwani ta shiga tsallake matan dake kwance. Aiko ta faɗi akan wata mace tim, ga uwani ba kaɗan ba. Matarnan ta saka ihu da kururuwa. "Haba baiwar Allah wannan ai iskanci ne, ji yanda kika faɗo mun so kike ki karyani?" Cike da fitsara take maganar gata yarinya ƙarama. Kiyi haƙuri baiwar Allah " Na faɗa ina daga tsaye. Ta bani amsa da cewa. "Babu komai. Sannunku da zuwa baƙi" Da ƙyar Uwani ta yinƙura da rarrafe ta isa waɗannan katifun biyu ta ajjiye jakar kayanmu ta zauna. Ƴar Ɗas ta dubeni tace. "Wannan tsaiwar ta babu gaira babu dalili dame yayi kama. Kin zo kin tsaya mun a ka, sai in tayar miki da aljanu Allah. " A tsorace na shige ƙofar dake kusa dani. Wani bayan gidane tsukukun gaske, komai dai tsab, ga ruwa a fanfo ga bokiti. Tuɓewa nayi na shesshiƙama jikina ruwan sanyi, dan a jiƙe kayana suke da sufa sharkab. Jiri da ciwon kai na yinwa duk yabi ya addabeni. Alwala na ɗauro na fito kayan dana cire su na mayar na saka hijabina na fito. Ƴar Ɗas tana zaune tana kallon ƙaramin mudubi na hannu. Uwani tsallako kije kiyo wankan" Uwani da tayi jigum tace. "Faɗuwa zanyi matsawar ban saka abinci a cikina ba. Bani da nutsuwar wanka, ki ƙyaleni kawai" Kai na girgiza dan nima yinwar shirin kayar dani take yi. Kafin ince wani Abun sai ga Taraliya ta buɗe ƙofa ta miƙo mun gurasa guda huɗu a hannu, da wani romon miya. Nasa hannu na karɓa ina jujjuya abincin. "Ku biyu ke da abokiyar tafiyarki. Ku yi da jiki maza, zaku fita yanzu da Hajiya Babba" Danƙarewa nayi a tsaye mamaki na neman ruguza nutsuwata. Da ƙyar naja ƙafata na tsalllaka na samu uwani. Loma shida gurasarnan tayi mun. Jima nayi kamar yinwar na sake tsokanowa wallahi gashi ko ruwa ba'a bamu ba. Sai Ƴar Ɗas muka roƙa ta bamu gora ɗaya ƙarama. Uwani daure ki je ki watso ruwa, ana binmu sallah fa, kuma kinga ance zamu fita." Uwani dai bata ce komai ba ta tsallake matan dake ta bacci hankali wance. Ƴar Ɗas dan Allah inane gabas, sannan a ina zanyi Sallah?" A yangance Ƴar Ɗas ta ce. "Ga gabas kin ganta. Batun inda zaki yi sallah kuma katifarki zaki jingine a bango kiyi sallah. In baki da dadduma sai ki shimfiɗa ɗankwalinki" Harna rama sallolin da ake bina hawaye bai dena zuba a idanuna ba, zuchiyata ta karaya ina hango mana wahala da wulaƙanci a gabanmu. Uwani itama katifar ta gingine ta soma rama sallolinta. Bata kai ga gamawa ba Taraliya ta leƙo kiranmu. Uwani bata idar da sallah ba Taraliya" "Tayi sauri ta sallame, dan Hajiya Babba ba'a ɓata mata lokaci. In ranta ya ɓaci baku ba cin abincin rana a cikin gidannan" Uwani tayi Sallama, ta dubi Taraliya tace. "Akwai sallar isha a kaina ban rama ba fa" Ƴar Ɗas tace. "Shawara ki tashi kuje, in kun dawo kya rama. Ba a yin musu da duk umarni. Ke wata rana ma kina ganin lokacin Allah zai shiga ya fice baki yita ba. Wata rana ma sai dai ki rama sallolin cikin dare a kulle a ɗakin da aka baki a matsayinki na ƴar aiki." Jikinmu na rawa cike da tsoro da tsinkewar zuchiya muka fice a ɗakin, kayanmu da jika. Haka aka turbutsamu a mota, wasu akan cinyar wasu. Duk wanda na kalla sai inga tana share hawaye, imma da mayafinta, imma da gefen zaninta. Zukata sun shiga damuwa da ruɗu. Wani gida aka kaimu, akaita mana aune, aune, bamu muka gama ba sai yamma lis. Basu bamu abinci ba, an dai raba mana ruwa munsha. Ɗakinmu muka tura muka shiga. Babu kowa a ɗakin, katifun dukka suna jingine a bango. Durƙushewa nayi ƙasa na sau kuka mai tsuma zuchiya da gangar jiki. Uwani na jan majina tasa hannu bibbiyu ta ɗago ni. "Iyabo tun a itofiya jikina ya mutu. Amman sai ƙara sama mana ƙarfin guiwa nake yi. Hankalina bai kai ƙololuwar tashi ba sai da muka shigo ɗakinnan mai kama da kabari. Muna cikin tsaka mai wuya a ƙasar da ba uwa ba uba, ba dangi." Kukane yaci ƙarfinta. Uwani mu dokara ga Allah. Allah ya ga xuchiyarmu mu neman kuɗi muka zo yi. Amman na fahimci kamar bayi haka aka ɗauke mu. Shawarar da zan baki, mu kai kukanmu ga Allah kawai. Da zamu samu hanyar komawa gida Najeriya ma da mun koma" Taraliya ce ta turo ƙofa, hannunta riƙe da gurasa kamar dai irin wadda aka saukemu da'ita. "To Wallahi kar ku sake ku sake ambaton Najeriya ma. In kuka kuskura wannan kalmar ta shiga kunne abokan zamanku, zasu isarma da Hajiya Babba. Ba zaku ji da daɗi ba. Sannan ku dena damun kan ku, ku da za'a tura gidan aiki. A can ɗaki sukutum za'a baku ku kaɗai a ciki. Kuma sai abinda kuke son ci zaku ci. Wannan zaman na ɗan lokaci ne. Ku dai Allah ya taimakeku ku samu shigewa da wuri. Dan naji Hajiya Babba na maganar gobe za'a soma raba ƴan aiki. Ku zauna kuci abincinku." Godiya Uwani tayi mata, har zata fita uwani tace. "Wai irin abincinnan kullum ake ci ne? Sannan wannan yayi mana kaɗan mu biyu" Dariya tayi bata ce uffan ba ta fice ta barmu a tsaye jigum. Jiki a saɓule muka rama sallolin da ake binmu. Muka lasa wannan abinci dan sai dai a kirashi da lasawa kawai. Muna zaune kowa dai da tunanin daya addabi zuchiyarshi. Yaya Hamma ne ya faɗo mun, dole na ɗan murmusa harma naji kwaranyar wani ruwa mai sanyi a zuchiyata. "Uwani ya kamata mu tambayi land line ɗin da akace akwai a ko wanne ɗakin ai. Ko dan ki samu ki kira mijinki ki sanar mishi isowarmu ko? Nima inason in kira Burodami in sanar musu da saukarmu" "Hmmm Iyabo mu nutsa mu gane kan gidan tukunna, kinganni yanzu haka yinwa kamar zata kasheni wallahi, gashi jikina ko ina ciwo yake yi mun kwanciya zanyi ko zan iya runtsawa a wannan halin da muke" Katifarta ta yar, ta ɗaura jakar kayanmu a katifarta, dan babu waje, kowa da kayanshi yake matashin kai. Ni dai ina zaune in tuno Dada, in Tuno Gwadabe, in tuno Ƴaƴana, in tuno Yaya Hamma da kuma Daso data haɗa zuchiyata da fargaba. A wajen a zaune bacci ya kwasheni ban sani ba kasancewar jikinmu a nune yake sosai, ga yinwa sai ta galabaitar dani. Allah cikin ikonshi sai da Asuba na farka, a ƙasa na kwana abina. Matan ɗakin namu wasu na kwance sunata baccinsu, yayinda wasu kuma suke Sallah, cikin masu Sallah harda Ƴar Ɗas, abunda ya bani mamaki shine banga Ƴar Ɗas da mayafi ko hijabin Sallah ba, banga kuma wannan yala_yalan gashin dana gani a kanta jiya ba, sai suma irin ta maza. Da Ɗan daudu muka kwana muka tashi ni Iyabo?" Na furta a zuchiyata ina mamaki, raɓewa nayi ta bayanshi na wuce zuwa toilet na ɗauro alwala. Ni dai har na idar da sallah ban dena mamakin Ƴar Ɗas ba. Sai hirarta take yi da mata ana tafawa, gata da barkwanci sosai. Ni dai naga matan ɗakin daga wannan mu ganta ta shigo da tea da biredinta, sai muga masu kaza gashasshiya, da masu wata doguwar shinkafa wacce ni tunda uwata ta haifeni banga shinkafa da kyau da tsarin wannan shinkafa ba, gashi taji naman kaza, ƙila itace shinkafa kaza da muke jin labari. "Bayin Allah ni ban gane ba tambaya ce dani dan Allah" Cewar Uwani data tashi tsaye. Ƴar Ɗas ta mike ƙugu a hannu yace. "Na taɓoki da alheri wai kishiya ta taɓa kishiya da bakin wuta. Faɗi tambayarki in rabtaɓo miki amsa, dan dana ɗumama cikina da kaza da laban kwanciya zanyi sai azahar kuma" Uwani tace. "Mu tunda muka zo wata bushasshiyar gurasace ake bamu, da wani romo da bamu san na meye ba. Bugu da ƙari ma ba isarmu yake yi ba. To sai kuma naga ku ko wacce da abinda ta saka a gaba tana ci, muna son ƙarin bayani." Ni kaina da Uwani bata yi musu wannan tambayarba, da ni zanyi musu. Yinwa tana addabarmu ainun, har ƙirjina ya soma nauyi. Ƴar Ɗas ya doki cinyarshi yayi juyi da ihu kafin yace. "Wannan gurasa da romo duk muma mun cita kafin mu yage rigar bauta, mu sa ta ƴanci. Duk wannan kayan ci na albarka da kike ji da gani, ko wacce da guminta na halak ta siya. In baki da kuɗi cin gurasa dole, batun ƙoshi kuwa kima fita zancan wannan. Kuma anan ba mai taimako wani, ko wacce ƙasarta ta baro ta fito biɗar kuɗin halak" Ɗayar matar mai Suna Madina ta dubemu ta ɗaura mana da cewa. "Idan kuka ƙara haƙuri da sannu komai zai wuce muku. Wuyarta ku soma aiki, kuɗi kam sai dai ku tura gida ma, abinci sai kun ture. Kunga irin baƙar azabar ni dana sha kafin in samu gidan aiki? Hmm abun yana da munin da ina faɗa muku zai karya muku zuchiya. Ku dai kuyi ta yin adda'a shine kawai" Taraliya ce ta miƙo mana wannan gurasa ta masifa. Sai dai yau matan ɗakinmu sun taimaka mana anyi mana karo_karo na abinci shine muka samu muka ji dama_dama. A taƙaice dai munfi kwana goma muna zaman jiran a kaimu gidan aiki. Anata ɗauki ɗaɗɗaya. Uwani da ƙyar ta samu lambar hajiyarsu ta shiga ta sanar da'ita isowarmu, sai ranar hankulansu suka kwanta da suka ji muna cikin ƙoshin lafiya,. A ranar aka tafi da Uwani gidan aiki, ranar nayi kuka kamar raina zai fita. Itama tana wannan kukan aka fita da'ita. Ni kaɗai na wuni ƙwalam a ɗaki, sai da nayi la'asar ne na shiga ɗakin dake jikin namu na tarad da su Hadiza suna ɗaki suma a zaune suna ɗan taɓa hira a tsakaninsu. "Iyabo kin leƙo ne, ina Uwani na ganoki ke kaɗai?" Cewar Hadiza. Tare da'ita muka tawo daga Kano. Sai da na zauna kana nace. Uwani ta tafi gidan aiki Hadiza" "To nayi mata barka wallahi muma nan duk zaman jiran hakan muke yi. Duk da ance aikin gidan larabawa ba ƙaramin aiki bane na azaba. Wasu fa wai har dukansu akeyi a gidan aikin." Idanu na zaro nace. "Yanzu Hadiza da girmanmu sai a kamamu da duka?" Dariya ma maganata taba ƴan dakin. Hadiza tace. "Hmmm Dattijuwar da take bamu wannan labarin kinga fa katifarta" Ta nuna mun katifarta a jingine" "Har bayanta ta nuna mana duk shatin bulala. Wannan dalilin ne yasa ta baro gidan aiki tana buƙatar a sauya mata gidan aiki. Duk matan dake cikin ɗakin ku fa da yawansu matsala suka samu a gidan aiki shi yasa kika gansu, za a nema musu gidan aikine" Ni dai jikina du yayi sanyi sosai. Na dubi Hadiza nace. In babu damuwa zan dawo ɗakinku Hadiza, can ɗakin namu basa zama, in suka fita sai dare, wasu ma sai su kwana biyu basu dawo ba" "Jeki maza ki ɗakko kayanki kinji, ai sai abun yayi miki yawa." A ɗakin su Hadiza kwanana biyar. Naji labarai masu tayar da hankali, da irin matsalolin da baƙaƙenmu suke fuskanta a gidajen aiki iri daban_daban kuma masu haɗarin gaske. Nifa tun daga Itofiya na soma ɗan daka ce ban baro ƙasara Najeriya ba. A ranar dana cika kwana goma a ɗakin su Hadiza nima akace in haɗo kayana waɗanda zasu ɗaukeni aiki zasu tafi dani. Hawaye na soma zubarwa da girmana, na suri ledar kayana, duban su Hadiza nayi da muka shaƙu a kwanaki gomannan nace. Allah ya sake sada fuskokinmu da Alkhairi, ni na tafi, ku taya ni da adda'a nima zan dinga yi muku" Ina kaiwa nan Taraliya ta figi hannuna zuwa wajen mota. Wata balarabiya da mijinta na gani a gaban mota, ni kuma Taraliya ta dannani a gidan baya. Motarnan na soma tafiya na runtse idanuna hawaye sai kwaranya yake yi a idanuna. Tafiya muka yi mai yawan gaske zuwa wani garin kuma. A cikin katafen wani ƙerarren gida motar ta tsaya. Ni dai ganin sun fito, nima saina ɓalle murfin motar na fito. Balarabiyar ta dubeni tace dani. "Yalla" Zungui_zungui dai haka naita binta a baya. Muka shiga wani ƙatoton falon da ko a mafarki ban taɓa ganin irinshi ba. Garjejen falone jere da wasu jajayen kujeru marasa ƙafa, duk da na kasa tantance kujerune ko fululluka manya aka jejjera oho. Duk girman falonnan kafet ne mamala a ciki, ga taushi, falon sanyi da ƙamshi yake fitarwa, ga matattakalar hawa bene daga can gefe, ga ɗakuna kusan goma a cikin falon. Ni dai ina biye da'ita zuwa wani ƙaramin ɗaki dage jikin matattakalar hawa bene daga ƙarƙashi haka. Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin tayi, da sauri wata dattijuwa baƙar fata ta buɗe, sai na ganta da atampa a jikinta, kuma tayi mun kama da Bahaushiya. Da larabci wannan balarabiyar tayi mata magana tana nunani halamar dai bayani take yi mata a kaina. Tana gamawa ta haura sama abinta. Wannan Dattijuwar tace.."Sannu baiwar Allah, da ganinki ƴar ƙasata Najeriya ce ko?" Tana faɗar haka saina fashe da kuka. Hannu tasa ta jawo ni cikin ƙaramin ɗakin. Mai ɗauke da gado mai hawa biyu, da katifa a jingine a gefe, sai tulin kayan sawa. A bakin gado ta zaunar dani tace. "Ki dena kuka yarinya. In dai arziki kika fito nema da guminki kin samu. Dan ana biya sosai a gidannan. Amman fa akwai aiki masu yawa sai kinji kamar zaki mutu. Bayana, ƙirjina duk ciwo suke yi mun. Aikin ya gagareni shine naima Hajiyar gidan magana inason zan koma Najeriya a samo wacce zata zama madadina. To gashi Allah ya kawo ki. Zan zauna dake na kwana bakwai in kula dake har sai kin gaggane aikin sai in tafi. Akwai wata yarinya itama aiki take yi da ɗayan shashin na gidannan. Amman ita bata jin Hausa daga wata ƙasar take. Yanzu bari in baki tea da biredi ki ci, sai in zaga dake ki kama aikin ki. Sunana Takarofi" Kukana na share, nace da ita. Sunana Iyabo" "Ayya beyerabiya ce ke ashe? Amman kinji Hausa sosai. Ina zuwa to" Fita tayi tana ɗingisawa, nabi bayanta cike da tausayawa sosai da ido. Bata fi minti goma ba sai gata niƙi_niƙi da kayan karyawa. Lafiyayyen biredi da kakkauran tea har da bota da wainar ƙwai. Cin haɗama nayi ma biredinnan. Takarofi sai kallona take yi. Bayan na kammala tsab sai tace in biyota muje. Nan ta zaga dani lungu da saƙo na gidan, da duk wani aiki da zan dinga gabatarwa. Time table na abinci ta nuna mun gasunan a rubuce reras da turanci. Ko wacce rana da irin abincin da za'a dafa. Cikin sarewa nace. Wai Mama dukka aikinnan ke kike yinsu ke kaɗai?" Murmushi tayi tace. "Shekarata biyar cib a gidannan ina aikin bauta. Ciwon baya, ciwon ƙafa da ciwon sanyi duk sun kashe mun jiki. Aiki zaki zage kiyi KAN JIKI KAN ƘARFI dan basa son saiɓi sai yanzu su koreki." Ajjiyar zuchiya na sauke, na shiga ruɗu da tashin hankali sosai. Nayi dana sanin baro ƙasata nace Kuma tsawon awa nawa kike ɗauka kafin ki kammala aikinnan har ki samu ki huta?" Dariya sosai wannan karon tambayata ta bata. Mrs Bukhari *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BOOK 2 8 "Iyabo. Abunda nake so dake shine ki kwantar da hankalinki sosai kiyi aikin ki yadda ya kamata. Kije ki soma wanke bayan gidun falon ƙasa dana nuna miki. Kiyi amfani da duk man wanke bayan gida dana nuna miki. In kin gama sai in koya miki yadda zaki yi shara da injin." Jikina a mace na gangaro ƙasa. Da wani gansamemen Balarabe naci karo a falo. Yana ganina sai yace dani. "Shayi" Yana mun halama da hannu da sha" Take na gyaɗa mishi kai na jiya kitchen ɗin. Tea spices Takarofi ta nuna mini na dafa na kai mishi yana zaune akan kujera. Nan na shiga aikina. Sai da na wanke bayan gidu takwas, tun daga bango har ƙasa. Ina fitowa na soma shara da injin ɗin shara, kafin in gama bayana ya ƙage dan azaba. Wani ruwan fesawa Takarofi ta bani da tsumma, haka na dinga bin bangon gidan ina fesawa ina gogewa yana ƙyalli. Na goge TV, TV stand, daining table da gilasan dake saman shi. Ina cikin haka na duba agogon falon naga lokacin sallah har ya gota. Gashi banyi wanke_wanke ba, ban ɗaura girki ba. Da sauri na koma ɗaki, Takarofi ta tare ni da cewa. "Lafiya na ganki afujajan?" Sallah zanyi" Agogo ta kalla, ta dawo da kallonta gareni tace. "Kin ɗaura girkin rana ne Iyaba?" A'a" Na bata amsa. "Iyabo muje kitchen ki samu ki ɗaura girki tukunna, ko a kitchen ɗin sai ki yi sallah. Ni kuma zan taimaka miki da wanke_wanken. Ƙarfe biyar yaran gidan suke dawowa daga makaranta baki gyara musu ɗakunansu ba,. Akan yarannan za'a iya korarki." Ni dai binta nayi zuwa kitchen ɗin. Sai da na tsayar da sanwar shinkafa kaza tsab sannan nayi alwala na shinfiɗa ɗankwalina na gabatar da sallah. Illahirin jikina babu inda baya yi mini ciwo. Amman haka na tashi ni ina gyaran kitchen Takarofi na wanke_wanke. Har dai girkin ya nuna aka juye a wata babbar kula ta silver, na jera komai a teburi. Kana na wuce ɗakin yara, a hargitse kaca_kaca ina hawaye ina aikinnan. Sai da na gyara ɗakin yara uku, ko wanne da bayan gida. Ina gamawa na faɗa ɗakin matar gidan na gyara, ɗakin mijinma ni na gyara. Bayan sallar magriba kuma muka fita ta bayan gidan da tulin wankin ja'amar gidan, Takarofi na koya mun yanda zanyi amfani da injin wankin. Hannuna tsabaragen gajiya rawa suke yi. A wajen wankin na samu nayi sallar magriba, a wajen naci abinci. Bamu muka gama wanki ba sai dab isha. Ga girkin dare zan ɗaura, ga wanke_wanken abincin rana, falonma yaran gidan da samarin gidan duk sun lalata. Haka na kuma gyarawa na ɗaura girki kitchen ɗin nayi isha na jejjera kayan abinci a daining yaran gidan da matar gidan suna falon suna kallon wani shiri a talavijin. Ina shiga nayi sallar isha ai sai zazzaɓi ya rabkeni, ko ina rawa yake yi a jikina abinci ma kasa ci nayi, Idanuna sai hawaye suke fitarwa "Iyabo ƙarfe tara tayi kije ki sama yaran gidan kayan bacci, samarin gidan kuma ki fito musu da kayayyakin baccin, ki kunna ma ko wanne ɗaki turaren wuta. Ga guga fa baki yi ba, ya kamata ki gama a darennan gobe ki tashi da aikin jerawa" Ai sai na rushe da kuka.. Haba kasheni za'ayi da aiki. Wannan aiki sai kace jaka" Kafin in rufe baki naji wata murya daga ƙofar ɗakinmu ana ambaton Sheika( ma'ana tsohuwa) A zabure Takarofi ta miƙe. "Taso Iyabo kinji daure" Da ƙyar na bi bayanta naje nayi duk abinda ya dace na dawo. Ina zaune sai guga nake yi. Zuchiyata kuma ta lula tunanin Yaya Hamma, da irin yadda muka rabu muna masu begen junanmu. Idanu na lumshe ina fata da burin in zama mata a gareshi. Sai da na gama gugar nan tsab nayi wanka na kwanta. Abinci ma na kasa ci sam. Ina kwanciya wannan yarinya da Takarofi tace itama ƴar aiki ce sai gata ta shigo. Bata jin Hausa bata jin turanci sai yaren Senegal. Ƴar senegal ce, sai gaisuwar kurame mu kai ma juna. Cikin bacci naji ana dukan kafaɗata, zabura nayi na zauna. Ƙirjina sai bugawa yake yi dana ga namiji a tsaye a kaina. Murmushi yayi mun yace mun. "Uridu an ashbu shayi ( zan sha shayi) Da Wata muryarshi mai zaƙin gaske. Na fahimci me yake cewa ta dalilin shayi daya ambata. A gajiye tulus na haura kitchen ɗin sama na je na dafo mishi shayin na kawo mishi yana zaune a falo. Ina harhaɗe hanya tsabar bacci da gajiya haka na isa ɗaki na faɗa gado ban sake sanin inda nake ba, sai da muka jiyo kiran Sallah. "Iyabo maza yarannan kije ki musu wanka su saka kayan makaranta. In kika ɗaura abincin karyawa sai kiyi Sallah " Bani da zaɓi haka dole na gabatar da abinda Takarofi ta faɗa mini. A kitchen ma nayi sallah abina. Zuwa shida da rabi na gama jera komai a daining. Har matar gidan, da me gidan sun fito. Cikin harshen turanci na gaishesu, suka amsa mun da "Sabahul Noor" Na juya na barsu nan. Da duku_duku na soma bi ɗakuna ina jera musu kayansu a durowa. Ƙarfe Takwas batai musu a gidanba, masu zuwa aiki sun tafi, ƴan makaranta ma haka. Tunda na shiga aiki banfa zauna ba sai ƙarfe biyun rana na kammala komai da komai, sai guga data rage mun kawai. Itama ina idar da Sallah na shiga aiki. Yau babu abincin rana, sai na dare, na dai dafa ma yara ƴan makaranta Taliya me kifi. Na cire musu kayan makaranta, nayi musu wanka, sai suka kwanta bacci. Ragowar abincin safe naci, farfesun kaza ne da dankalin turawa, sai dafaffiyar madara. "Dake da ƙwarinki kinga har kin gama aikin ki ƙarfe huɗun yamma. Aikin yayi sauri sosai. Ina mayar da numfashi nace. Amma Mama azabar tayi yawa. Wannan aikin ai dole ya illata jikin mutum, bautar tayi yawa. Ace in ka tsaya a tsaye tun duku_dukun asuba ba kai zaka zauna ba sai huɗun yamma. Shima biyar nayi zaka tashi ka shiga hada_hadar girkin dare. Ba kai zaka samu kanka ba sai kusan sha ɗayan dare." Takarofi tace. "Wannan aikin shi ya fiye miki alkhairi. Duk yarinyar da bata zaune a gidan aiki, to yawon ta zubas take yi a gari. Kinga kuwa ai zaman gidan aikin ya fiye mata ko?. Sannan inaso in ja kunnenki in gargaɗeki. Kinga gidannan akwai Samari har su shida majiya ƙarfi. Kibi a hankali dasu, a kullum in zaki shiga ɗakunansu ki yi adda'ar neman tsari Allah ya kareki daga sharrinsu. Dan suna shigo da matan banza cikin gidannan. Naga kuma ke yarinya ce, ki tsare darajarki tunda ba abinda ya kawoki ba kenan." Shiru nayi ina nazarin kalamanta hankalina ya tashi ainun, lallai ina cikik tsaka mai wuyar fita. Wannan ai shi ake kira gidan tara. Girman gidan na soma hasasowa, da yanda nake marar ƴanci a cikin gidan. Taya zan ƙwaci kaina daga wannan sharri. Ni kaɗai a gida sai samari garada, shin in ihu nayi wazai kawo mun ɗauki ma?" Na shiga tsaka mai wuyar fita. Tunanina sai ya koma gida Najeriya. Bani da wani buri daya wuce in koma ƙasata in ci gaba da rayuwa a cikin ƴanci" Wannan tsoro da fargaba sai suka samu muhallin zama daram a tattare dani. A ranar dana cikata kwana bakwai a ranar Takarofi na tayata ta haɗe kayanta tsab. Matar gidan tai mata goma sha tara na arziki. Ni dai ina kuka muka rabu da Takarofi. Damuwa da fargaba sai suka aureni. Na wuni ina bauta, da daddare kuma tsoro ya hanani bacci. Ɗayan shashen na zuchiyata bashi da aiki sai begen Yaya Hamma. A duk dare da rana tunaninshi ne ke ɗan bani wani nutsuwa da samar min da guntun farin ciki. A baya na faɗa muku ni zuchiyata bata iya son abuba sam. Soyayyar Yaya Hamma muhalli sosai ta samu a zuchiyata. Dana tuno siririyar fuskarshi mai ɗauke da fararen idanu take Sai inji baƙin ciki ya yaye mun. Amman fa son Yaya Hamma bai taɓa matsayi da darajar Gwadabe a zuchiyata da rayuwata ba. Kawai dai ina ƙoƙarin binne sonshi ne in fuskanci alƙiblar da take daidai. Ko da zamu dawo aure misali da Gwadabe, dole sai na auri wani namijin kafin hakan ta faru. Balle bana fatan Abinda zai sa in sake kai kaina inda basu san matsayina da kimata ba." Haka dai lokaci yai ta tafiya, tunani a ko da yaushe shine abokin hirana. Dan ni da Malika bama iya hira sai dai maganar kurame kawai, kuma in ta tafi ɓangaren da take aiki bata shigowa ɗakin baccinmu sai goman dare. A mugun gajiye take shigowa, to a haka ne muke ɗan taɓa hirar da bata wuce ta minti biyar ba. Wasa_wasa watana uku a gidan aiki. Duk wata wahalar aiki, da hawa da sauka ta zame mun jiki. Kullum a cikin ciwon baya dana ƙirji nake. Abinci wannan bani da lokacin da zan cishi a cikin nutsuwa, in aiki ya caɓe mun ma sai in wuni banci komai ba. Gashi a cikin kwana biyunnan kullum sai Khalifa ya shigo ɗakinmu da daddare. Sai ya taɓa jikina a kullum in zai tasheni daga bacci. Dana soma bacci sai inji mutum a kaina. Shayi dai shayi dai. Da yana zama a falo ne in dafa in kawo mishi. Amman yanzu sai yayi komawarshi ɗakinshi dole inna dafa in shiga in kai mishi. Kullum da mace a gadonshi, babu ranar dana taɓa shiga banga mace a ɗakinshi ba. Wataran tun daga ƙofa zanci karo da rigar mama da ɗan diras a ƙasa. Haka zan ajjiye in juya. Irin kallon da yake bina dashi shi yafi komai birkita lissafina. Dalilin da ya soma sani rama kenan. Yau tun safe na tashi da faɗuwar gaba da ƙunci. Ko dana shiga kitchen ɗora abinci sai na yi zaman dirshan na saki kuka. A mugun takure rayuwata take, zuchiyata babu daɗi kaɗaici na neman haukatani. Baka da wanda zaka yi magana kaji daɗi. Baka da lambar ƴan uwanka balle kaji muryarshi ko zaka ji sanyi. Akwai number Burodami Debisi, amman Uwani ta haɗa a kayanta ta tafi dashi. Daga kaina naji ance. "Maaza?" ( Menene) Ina ɗagowa muka haɗa ido da Khalifa. Ganin hawaye a fuskata caɓe _caɓe yasa shi saurin miƙi hannunshi yana son ya share mun. Da mugun sauri na miƙe na fita da gudu a kitchen ɗin. Baya na fita naje na saka wanki a injin jikina har rawa yake yi mini. Dana dawo kitchen ɗin na tarar baya ciki. Ajjiyar zuchiya na sauke, kana naci gaba da aikina. Sai na sake tsananta adda'a nice kullum cikin tsaiwar dare ina roƙon Allah ya tsare mun mutumcina, Allah kar yaba kowa damar iya tunkarata dai dai da maganar iskanci. Kullum cikin kuka da miƙa lammurana ga Allah. Khalifa bai daina shigowa ɗakinmu tsakar dare ba. Sai dai kullum zai shigo ya same ni ko ina sallah, ko da carbi a hannuna dai. Wasa_wasa lokacin sai tafiya yake yi. Yau da gobe rayuwa sai garawa take yi. Kamar wasa yau wata na shida cib a gidan aiki. Yau na tashi da farin ciki marar misaltuwa. Uwar ɗakina ta faɗamun tun jiya akan in shirya zanje ( Ijaza) Ma'ana zan tafi hutu can Riyahd. Tun safe na gama aiyukana tsab. Misalin ƙarfe Takwas na Safiya muka kama hanya, harda Khalifa ni dashi muna bayan mota, Uwar ɗakina da mijinta suna gaban mota. Zuchiyata a cike take dam fa farin ciki da ɗaukin son tozali da Uwani. Ko ba komai mayi hira muji daɗi ai. Tafiya mu ka yi sosai, ni sai yau ne naga nisan wajan sosai. Muna isa bakin kofar gidan na gane gidanne. Khalifa ne ya miƙo mun wata takadda a cikin gidan saka wasiƙa. Yaimun nuna da idanunshi akan in karɓa. Hannu nasa na amsa ni dai jikina bai bani ba. Tare da ƙunshin kayana dama nake. Sallama nayi da uwar ɗakina anan take shaidamun nan da sati guda zata aiko khalifa ya dawo dani. Cikin zumuɗi nake ta haura benen, sai dai bayana wani irin riƙewa yake yi tamkar bayan tsohuwar data gaji da duniya. Ina yi ina hutawa harna ƙaraso hawanmu. Ɗakin da Hajiya Babba take na soma shiga. Naje na sameta da baƙin wasu Larabawa da nake tunanin masu ɗaukar ƴan aiki ne. A wulaƙance ta amsa gaisuwata, abun ya dake ni sosai, domin wulaƙanci ba abin so bane. "Ke kika matsa musu kina son kizo hutu ko? Dan uwar ɗakin ki ta kawo ƙararki har sau biyu. Tace baki da aiki sai kuka. Dukanki suke yi, ko wani abun yaran gidan suke miki? Gashi naga kin lalace har kinfi kyau sanda kika tawo daga Najeriya" Duk wannan maganganun cikin ɗaga murya da harara take yinsu. Ajjiyar zuchiya na sauke tare da cewa. Ina zaune tace in shirya zanje Ijaza, ni ba roƙo ba. Maganar kuka kuma damuwa da kaɗaici ne suke sani kokawa, ai bawa ba'a iya rabashi da kuka. Imma na farin ciki, ko kishiyar hakan" "To uwar tsari. To zan kirata inji Allah yasa ba sallamarki tayi ba. Kin samu gidan mutanen kirki, duk cikin ƴan uwanki da kuka tawo daga Najeriya albashinki yafi nasu tsoka. Wata huɗu ya rage miki ki gama biyan kamfani kuɗinsu, daga haka kuɗi zasu dinga zuwa hannunki ya rage naki kisan yanda zakiyi dasu." Jin wannan daddaɗan labarin ya sani a farin ciki dan haka da murna na fita a ɗakin zuwa ɗaya daga cikin ɗakunan. Ina buɗewa naga Hadiza na kwance tana hutawa. Ganina yasa ta washe bakinta. "Ƴar halak kin ƙi ambato. Ko awa guda Uwani bata yi da yin maganarki ba sai gaki" Zama nayi a katifar dake kusa da tata. Uwani tazo kenan yaushe?" Na tambayeta. "Ai inajin zata kwana biyar haka. Tama kusan komawaa da rabon zaku gana ne, ni gobe ma zan koma" Gaisawa mu kai da juna. "Iyabo wannan rama haka. Kaddai kema a cikin tsaka mai wuyar fita kamar ni kike?" Ajjiyar zuchiya na sauke nace. Hadiza a tsaka mai wuya nake. Ni fa a gidan aikin da nake ko baccin kirki banayi, sabida bargaba, ga aiki kamar zan mutu, bayana da ƙirjina ciwo suke yi" Hadiza ta share hawayenta tace. "Talauci da neman na rufa ma kai asirine ya kawo ni wannan ƙasa. Akwai wata ƴar maƙotanmu bazawarace bayan ta baro gidan mijinta sai ta tawo Saudiyya aiki. Iyabo a cikin shekaru biyu kacal iyayenta suka sauya, mahaifinta har mota yake ja, gashi ta gyara musu gidansu. To shine mahaifiyata ta matsa mun akan nima in tafi, haka na bar mata yaron da nake goyo na tawo. A gidanma nike aikatau ina lura da marayun ƴaƴana da iyayena. Sai gashi a gidan aiki saurayin gidan har wuƙa yake nuna mun, akan sai na bashi haɗin kai. To bani da zaɓi dole haka na bashi haɗin kai yake biyan buƙatarshi dani dan dole. Gashi ni bansan hanya ba bare in gudo. Iyabo na dawo Ijaza sai nake sanarma Hajiya Babba halin da nake ciki akan a sake mun gidan aiki. Hmm kar ki so ganin zagin tsaman naman da tayi mun. Da ƙyar ta yarda akan za'a sake mun gidan aiki. Ni gobe zan kama wani aikin." Kukane da tausayinmu gabaki ɗaya yake shirin cin ƙarfina. Haƙiƙa na tausaya ma Hadiza matuƙa gaya. Dan kawai kana aiki a ƙarƙashinsu sai su nemi tilasta maka akan abinda sun san haramcinshi. Taya yaron gida zai hakkema mai aikin gidansu, dan kawai ta tawo ƙasar da ba tata ba, tana neman guminta? Ya Allah ka dubi bayanka ka kawo mana ɗauki. Allah kasan zuchiyarmu ba iskanci ya kawo mu wannan ƙasa ba, neman kuɗi ne ya kawo mu ya Allah ka karemu da karewarka. Hadiza na tausaya mana duka. Ni kaina ayau ba sai gobe ba zan faɗa ma Hajiya Babba inason sake gidan aiki. Tun kafin Khalifa ya samu nasarar keta rigar mutuncina. Yaron gidan da nake aiki ne yake kawo mun hari. Kullum bashi da aiki sai kawo kala_kalan ƴan mata" Hadiza ta share hawayenta tace. "Gara mu sake gidan aiki. Ko Allah zai sa mu yi dace da irin gidan da Maryam ta samu. Baki ga Maryam ba yadda tayi kyau ba. Gashi da zata tawo Ijaza sababbin abayoyi aka sai mata gwanin sha'awa" Ɗan murmushin tausayinmu na kuma yi. Uwani ina suka je ne?" "Hmm sun tafi miƙe ƙafa da ganin gari ita da su Maryam. Uwani ma baki ga ramar da tayi ba, juyin duniya taƙi faɗin matsalarta sai kuka ba dare ba rana" Ana cikin haka p'a ta rako wasu mata su huɗu, ƴan ƙasata najeriya biyu, sai ƴan nijer suma su biyu. "Iyabo ijaza kika zo yaushe banga shigowarki ba?" Ɗan murmushi nayi na miƙe muka fita da p.a Yanzu zuwana p.a Hajiya Babba ta sallami baƙinta kuwa?" "E sun tafi yanzu haka ma Airport take son tafiya zata ɗebo baƙin Najeriya. Ince dai ba cewa zakiyi a sake miki gidan aiki ba, dan abinda Hajiya Babba ta tsana kenan." Kai na girgiza tare da cewa. Gidan aiki kam zan canja, domin samun tseratar da mutuncina. Ni bazawarace ina da yara har uku, ga iyaye da ƴan uwa. Ai bazan so in ɗebo musu abun kunya ba, daga zuwa aiki, in bari tarbiyata ta taɓu ba" Murmushi p.a tayi mun tace. "Wani hanzari ba gudu ba Iyabo. Da dirinki da kyanki ni nayi mamaki ma da kika zauna a gidan aikatau harna tsawon wata shida. Nayi tunanin harkar samun maƙudan kuɗi cikin sauƙi shi zaku ɗauka daga ke har Uwani na ganku tubarkalla. Da a fita ɗaya ma zaku biya bashin da kamfani take binku, kuma ku zama ƴan lele a wajen Hajiya " Da mamaki na dubeta. Dama akwai hanyar da ake samun kuɗi cikin sauƙi shine ba'a nuna mana ba?" Dariyar cin nasara p.a tayi mum ta dafani. "Yanzu ki koma. In Hajiya Babba ta fita zanzo ɗakinku mu tattauna kafinnan Uwani sun dawo" Da wannan zancan muka rabu da p.a. Ina juyawa da zummar komawa ɗaki na jiyo muryar uwani. "Iyabo" Ta kirayi sunana. Da sauri na juyo muka haɗa idanu, ba ƙaramin ramewa Uwani tayi ba, sai naga tayi wani irin haske. Take gabana ya faɗi. Tana ƙarasowa muka rungume juna sai kuka kamar ƙananun yara. Su maryam kuma su kai shigewarsu. Ɗago Uwani nayi na riƙe kafaɗarta. Uwani kin rame da yawa. Sai naga kinyi ɗanye kamar me yaron ciki" Sai ta sake fashewa da kuka. Ɗakin da babu kowa a ciki ta jani muka shiga. "Iyabo ina cike da nadamar baro ƙasata Najeriya, ina mai cike da fargaba da tashin hankali marar misalin da za'a musalta balle har a fahimta. Iyabo ciki ne dani na tsawon wata biyu" Da sauri na toshe mata bakinta tsabaren tashin hankalin dana tsinci kaina a ciki. Matar aure da cikin da bana mijinta ba Na faɗa a cikin raina, a fili kuma nace. Uwani baki faɗa mishi ke matar Aure bace to?" "Na faɗa mishi da kwaɓaɓɓen turancina. Amman Iyabo yaƙi yarda. Kullum cikin dare sai ya baro matarshi yazo ya tare a ɗakina. Kuka da majiya baya hanashi aikata komai. Na dawo da tarin kuɗin da bansan iyakar yawanshi ba. Musamman da nace mai cikine dani. Ya bani kuɗi masu yawa yace in na tafi kar in dawo, in matarshi ta gane shi yai mini ciki dani dashi zata haɗa ta kashe. Iyabo abinda bakai da ƙuruciya ba, sai da aure a kan ka. Me zance da Hafizu, me zance da su Hajiya?" Kukane yaci ƙarfinta. Niko sai kallonta nake yi ina auna girman abun. Cikin dauriya nace. Da Hadiza tace jibi zaki koma, can gidan kike son komawa?" Kai ta Girgiza. "Inata tunanin ta hanyar da zan ɓulloma da Hajiya Babba ne. Naga irin ɗibar albarkar da taima Hadiza data buƙaci sauya gidan aiki. Ni Iyabo yaya zanyi da cikinnan?" Wallahi Uwani ban sani ba, ƙasa ba taka ba. Amman bari Hajiya Babba ta dawo, ya zame mana dole mu tunkareta ko dafamu zata yi taci. Ki share hawayenki Allah zai kawo mana mafita. Taso mu koma cikin mutane" Hannunta na kama muka koma ɗakinsu Hadiza. Duk cikinmu in aka cire Maryam babu wacce take walwala, sai kuma baƙi da basu san dawar garin ba. P.a ce ta leƙo ta yafitoni ni da Uwani. Ta shigar damu wani ɗaki kamar na ajjiyar kayane haka, amman da halamu anan ita take kwana. "Ku zauna ga katifa" Zama mu ka yi kamar yadda ta umarcemu. Cikin sakewa p.a ta soma yi mana bayanin da tuni ya kwance lissafi da notikan kaina. Uwani kuma sai hararar p.a take yi. "To harkace ta arziki tasa na kira ku. Matsawar kuka amince da abinda na kawo muku wahalarku tazo ƙarshe. Ai kamarku kun girmi gidan aiki sai dai a haɗaku da manyan alhazzai, ko manyan hajiyoyi da zaku dinga ban gisiri in baka manda. Ku ba yara bane kun dai gane wannan lissafin ai " Uwani ta balbalin ta miƙe cikin jaraba da nasifa tana nuna p.a "Mu rasa a ƙasar da zamu yi iskanci har sai mun zo Riyahd a inda muke jin ƙamshin ɗakin Allah. Kuma har kike mana tayin maɗigo? Ta Allah ba taki ba Allah ya tsaremu da sharri irin naki tur da tsufa da furfurarki dattijuwar biri. Iyabo muje kinji kafin in hallasa in kashe matsiyaciya." Jikina a mace na miƙe muka fice. Fitar da tayi dai_dai da dawowar Hajiya Babba da tarin mata. Matan aure da ƙananun yara da ƴan bana bakwai. "Sannu da dawowa Hajiya Babba" Uwani ta faɗa a tsorace wani kallon uku saura kwata tai mana dai dai fitowar pa. "Ince dai lafiya ko?" A'a ba lafiya akwai gagarumar matsala" Nayi maza nace. Kallonmu tayi, ta kalli jama'arta da su kuma daka gansu a galabaice suke. P.ai ki ji da waɗannan ayi musu yadda ya dace. Ku kuma mujenku." A baya muka bita izuwa inda take ganawa da baƙinta. Labarta mata halin da Uwani take ciki nayi, da halin da nake ciki a nawa gidan aikin. Tare da roƙon a sake mana gidan aiki, kuma ta taimaka a zubar da cikin jikin Uwani. "Lallai na ɗebo jagwal, ko kuma in kiraku da ƙaƙai. Kusa kunnuwa da kyau a garinnan ganin maganin zubar da ciki ai aikine jajazur. Za a iya kamaku ma matsawar kuka zubar da cikinnan. Wata shida da kama aikinku sai tarin matsaloli. Shi wanda ya ɗibga miki cikin yasan abinda ya aikata kin faɗa mishi?" MRS BUKHARI Tofa wasa farin girki. *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* Masu neman ƙarin bayani saiku tuntuɓeta 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 9 "E ya sani, harma ya bani kuɗaɗe yace inna tafi kar in dawo dan in matarshi ta fahimci shi yaimun ciki zata kashemu dukka" Dariya Hajiya Babba ta kwashe dashi ta ɗauki waya ta daddanna, jim kaɗan ta soma larabci tana faɗa ta inda take shiga ba tanan take fita ba. Ajjiye wayar tayi tana tsaki. "Ku tashi ku bani waje, yace zai kawo miki maganin zubar da cikin zuwa gobe. Sai ki zauna da shirinki. Ke kuma zan duba lamarinki, ku tashi kuje" Ni na tallafama Uwani ta miƙe jikkunanmu a mugun mace, haka wunin wannan ranar ya kasance mana cikin tubka da warwarar al'amura. Yaya Hamma na tuno da irin kishinshi. Take na lumshe idanuna hawaye suka gangaro mun. Yarana na kuma tunowa da ubansu. Take murmushi ya suɓuce mun. Takaddar da Khalifa ya bani na ciro a ledar kayana na farketa. Kuɗine sababbi suka zubo masu yawa a mimmiƙe. Uwani ta dubeni tace. "Wannan kuɗaɗen fa Iyabo?" Hmmm Saurayin da nake faɗa miki Khalifa na gidan da nake shine ya bani da suka saukeni a ƙofar gidannan. Uwani baki bani labarin wuyar aikin gidan larabawa ba." Ɗan murmushin dole tayi mun tace. "Sawun giwa ne ya take na raƙumi. Amman duk wata azaba ta tabbata a aiki a gidan larabawa. Wuni guda cur mutum a tsaye kamar jaki. Sallah ma sai kayi da gaske kake ƙwacewa kayi. Iyabo abun babu sauƙi ni duk ƙasar ta isheni gida nake son komawa. Hafizu kuma baya nan yana can Canada ko a wanne irin hali yake sai Allah. Dan ba mui waya dashi ba hajiyarmu ce take faɗa mun. Sai hankalina ya koma gida. Ya kamata ki kira Burodami Debisi kema ai." Baki na taɓe nace. Wannan rayuwa cike take da ƙalubale Uwani. Sai yanzu nake dana sanin ƙin bin shawarar Yaya Hamma da Burodami. Yaya Hamma har shanu ya siyar ya bani jari in dinga zuwa kano ina sare_sare amman wallahi naƙi fur, sabida ni manyan kuɗi nake hari. Uwani shekara na zagayowa ni dai zan tafi gida magana ta gaskiya, da dai na samu ƴan kuɗaɗen juya kasuwanci, da ɗan kuɗin da zan saima Dada ɗan gidan da zata zauna shikenan ni daman ba wani abun nake nema ba. Bani number Burodami in kira ko zan sameshi" Jakarta ta buɗe na hango kuɗi sosai a saman jakar, takaddar da na rubuta lambar ta miƙo mun, na daddana number, na kira ta ƙaraci ringing babu wanda ya ɗaga, na sake gwadawa bata sauya zane ba. Anƙi ɗaga wayar Uwani, zuwa gobe na sake gwadawa . Washe gari da safe muna kan karyawa sai hira aketayi a ɗakin. P.a ce ta leƙo tai kiranmu baki ɗaya ni da Uwani. "Tashi muje Iyabo. Kinsan halin almurar matarnan bata da daɗi sam." Tashi nayi ina lashe hannuna muka je muka sameta da wani mutumi a zaune a kujera. Ashe shine wanda yaima Uwani ciki. Magani Hajiya Babba ta miƙo ma Uwani a farar leda. Jikinta na rawa ta amsa. "Ga maganinan na zubar da ciki. Ɗaya zaki sha, sai ki tura biyu gabanki. Ki jirayi zubar jini minti talatin da sha. Sannan ya bada kuɗi wanda har yafi ƙarfin kuɗin da nake binku ke da ƴar uwarki. Amman ki sani sisin kwabo ba zaki gani ba, wanda ya baki ma in kika bani haɗawa zanyi in karɓe. Ku shirya Zan mai da ku Jidda kuci gaba da zama. Dan yana buƙatar kiyi nesa da garin da yake, dake da wanda ma ya sanki. Dan haka kuje ku ɗebo kayanku yanzu mu wuce, kamfani bata binku ko sisi, sai kuje ku nemi kuɗi a Jidda." Kasa magana mu ka yi dan takaici, da mamakin zalunci irinna Hajiya Babba. Haka muka ɗakko kayanmu, mu kai Sallama dasu Hadiza, nan muka kama hanyar Jidda. A wannan gida na Jidda anan muka ga abubbuwa na tashin hankali, anan muka ga masu ciki iri daban daban. Yaranmu sun zama wasu ƙananun ƴan iska, yarinya ƙarama da buɗaɗɗen idanu. Sai girke_girke wasu daga cikinsu suke ta faman yi. Abun mamakin ma abincin gida Najeriya suke dafawa, dangin dambu, shinkafa da wake. Can gefe kuma ga wasu tsofaffin mata sai ƙulla gyaɗa soyayya da aya suke yi. Sai yima Hajiya Babba sannu da zuwa suke yi. Ni dai ina riƙe da hannun uwani dam. Duk inda Hajiya Babba ta cire ƙafa anan muke ɗora tamu har zuwa wani ɗaki mai cike da kayan more rayuwa. Sai wasu dilolin kaya a zube a tsakar ɗakin da halama na siyarwane. Wata tsohuwar ƴar duniya muka tarar a kwance tana waya sai zabga larabci take yi tana dariya. Bayan ta ajjiye wayar ta dubi Hajiya Babba tace. "Waɗannan sune matan da kika ce zaki kawo ɗin" Hajiya Babba tace. "Gasunan kin gansu. Duk abinda kike ganin ya dace a kansu ki zartar kawai. Kinga me juna biyun ita dai za a iya jefata a kasuwanci dan Abu Khadija ya faɗamun ya bata wadatattun kuɗin da zata lura da lafiyarta. Ita waccan ko gidan aiki ne sai ki jefata, Allah bashi in ta tara kuɗinta ko kasuwancin tura kaya Najeriya ne sai ta soma itama. Tunda dai sun biya kamfani kuɗinta. Ga fasfo ɗinsu nan" Ta zuge jakarta ta ciro ta miƙa ma wannan mata. Kallonmu tayi tace. "Ke me juna biyu, kina da sha'awar kasuwancin tura gumama gida Najeriya ire iren dogayen riguna haka?" Ta nuna mata na zube a tsakar ɗakin. Kana ta ɗaura da cewa. "Harkace mai riba sosai, domin a Najeriya da tsada ake siyen dila. Da sai ki soma ko da da dila ɗaya ne kina turawa gida. Da zaran kinga harkar ta karɓeki sai ki dulmiya kuɗi a dama dake. Ga harkar zannuwan gado, ga harkar barguna ma itama tana tafiya( Anty Zee me zanin gado ana magana) ga atampa ƴar leda matan Najeriya na sonta sosai." Uwani dai ita damuwarta cikin dake jikinta ne, kuma a zahiri tana son taimakon iyayenta sosai. Kuma tasan mahaifiyarta ƴar kasuwace zata tsaya tsayin daka ta siyar da kaya in an tura mata yadda ya kamata. "To Hajiya kamar yadda kika ce sai in soma da dilar gumamar mu jarraba. Itama ƙawata bata buƙatar gidan aiki. Tana da kuɗi inma ba zasu isa ba, in nawa zai kai a sai mana dila biyu shikenan sai a siya mana. Mahaifiyata zata dinga siyar mana ana turo kuɗi muna tura wasu kayan." Hajiyarnan tace. "To da zafi _zafi ake dukan ƙarfe tunda dai da kuɗaɗenku dilolima akwaisu iri da kala a gidannan. Zan kaiku ku zaɓa sai ayi batun kuɗi. Sabida jirgin kayan ana ɗan samun jinkiri zaki ga bai isa da wuri ba. Kuma za a iya saro muku kaya daga can gida Najeriya kuma kuci kasuwarsu. Zaku fi ganin afkin kuɗin." Nan dai Uwani ta fito da kuɗi aka haɗa da nawa duk muka ɗungume kuɗi muka bata. Ashe wannan shine somin shigarmu cikin tarin tulin matsaloli. A taƙaice dai ashe damfara ce kawai Hajiya Babba ta haɗa domin ta karɓe wannan kuɗi da shi Abu Khadija da yaima Uwani ciki ya ambata mata ya ba ita Uwani. Gashi a gidan haya ake biya, kai zaka sai abinci da kuɗinka, kai zaka sai sabulun wanki da abun goge baki." Uwani dai tana kwance tana jinyar jikinta dan ta sha ciwon cikin da harna fidda rai da ci gaban rayuwarta. Cikin hikimar Allah kuma sai ya tashi kafaɗunta a cikin kwana na goma da zuwanmu gidan. Abinci bashi nake karɓa mana a wajen masu abincin gidan. Ƴan cirani babu irin waɗanda babu a gidan. Har mabarata mata da ƙananan yara akwai. A kwana na goma sha biyu sai gani a titi ina faɗin sabil_sabil ina kuka. Hajiya Zuwaira macece maras mutunci da rashin tausayi a hakan tazo take tambayarmu kuɗin hayar ɗaki wai kwana goma_goma ake biya. Watsi tayi mana da ƴar jakar kayan namu. Sai Fati wata yarinyace ta taimaka mana muka dawo ɗakinta. "Sai fa haƙuri. Amman me zai hana ku nemi gidan aiki. Tunda dai ba zaku iya irin rayuwar da mu muke yi ba, muma ƙaddara da wahalar aiki a gidan larabawa ne ya ja mana, kuma sai ka fi shekara nawa baka tara wani abun arziki ba. Ai ina ganin zai fi muku ko?" Ina sharar hawaye nace. Na amince zan tafi gidan aikin Fati. In shekara ta zagayo sai mu koma ƙasarmu abinda muka tara Allah ya amfana." Nan muka amince Hajiya Zuwaira ta sama mana gidan aiki. A can wani gari me nisa. Ni na soma tafiya wannan karon. Gidan wasu tsofaffin miji da mata aka kaini. Gidan akwai tarin aiki, ga tsofaffinnan da tsari, gasu da yawan yin baƙi. Haka na kama aiki ka'in da na'in kullum mafarkina bai wuce in buɗe idanuna in ganni a gida Najeriya ba. Ga dakon soyayyar Yaya Hamma da zuchiyata take ta faman ɗawainiya dashi. Duk tarin gajiya da tarin matsaloli daidai da sakan zuchiyata bata taɓa barin tunanin Yaya Hamma ba. ( Ina kira ga mata masu tsallake ƙasarsu su tafi wata ƙasar da zummar yin aiki. Ku sani in kinga wata taje ta samu kuɗi baki san irin sana'ar da take yi ba harta samu wannan kuɗin ba. Wasu har rasa rayukansu suke yi. Wallahi babu iriyar azabar da ba'a ganawa waɗannan mata masu barin ƙasarsu zuwa wata ƙasar. In baizo kanki bane kawai zaki ga kamar duk waɗannan abubbuwan basa faruwa. Amman akwai da yawa waɗanda suka shiga tarin matsalolin daya dama na su Iyabo ya shanye. Amman fa bance ba'a dacewa ba. Wasu suna iya zuwa saudiyya su ƙaraci rayuwarsu a gidan aiki ɗaya ba tare da sun sake ba. Kuma in har za a rabu ma kiga iyayen gidan sunyi ma ƴar aiki kyautuka na alfarma. Ƙalilanne masu dacewa da hakan. Da yawan yaranmu in suka tafi lalacewa suke yi su shiga harkar banza. Ke uwa, ko miji kuna gida gaho damuwarku ayi muku gini, a dinga turo muku kuɗi. Baku damu da halin da yaranku suke ciki ba. Kuma da yawan agait agait ɗinnan da yawansu basu da kirki cuta da ha'inci kawai suka saka a gaba. Da kin taɓasu sai suce suma hakan akayi musu. Ƙalilanne daga cikinsu zuchiyarsu take a tsabtace.) Gaga_gaga haka rayuwar tayi ta faman tafiya. Aiki kamar zai kasheni. Ba hutu, ga ciwon baya mai tsananin gaske da nake fama dashi. Musamman wayewar garinnan ta yau. Nama kasa miƙewa sallar asuba ma sai a zaune nayi. Gashi uwar ɗakina yarinyarta dake aure a Madina suna gidannan ita da yaranta huɗu tazo duba mahaifiyarta. In miƙe tsaye fa na kasa. Wallahi Allah sai da rarrafe na samu na fito. Ina ganin Uwar ɗakina na fashe da kuka nake cakuɗa mata larabci ina kwatanta mata zanje gida bayana ba lafiya. Hankalinta ya tashi. Take ta taso ƴarta aka ɗaukeni zuwa gida. A lokacin watana biyu da zuwa gidan kenan. Da ƴan kuɗaɗena a lalita dasu nake kwana kuma dasu nake tashi. Fati ce ta samu tawul da ruwa ta dinga dannamun bayan nawa, wanda a wannan lokacin har kumburi yayi. Ta mulke mun bayan da man zafi. Sai sannu wani ɗan daudu yake yi mun ƙawar Fatyne. "Subhanallaah ni kam ku rufa mun asiri kar ki mutu muna ɗakinnan ki jaza muna jafa i" Haƙorana suna kakkarwa nace dashi. Dama mutuwar zata zo ta ɗaukeni kaga shikenan nima na huta." Sai yayi shiru, can kuma yace . "Kinma ci abinci kuwa" Kai na girgiza mishi halamar A'a. "Kawo kuɗi a haɗo miki tea ki ɗumama cikinki, sai a ɗan haɗo miki da farfesu" Gudun kar susan akwai kuɗi a jikina, domin na fahimci rayuwar Saudiyya ba wanda yake yarda da kowa sai nace. Faty Ki ranta mun, dana samu dama_dama zan baki kuɗinki dan Allah" Cikin minti talatin sai gata da shayi me kauri da farfesun kaza, naci sa a na samu naman ƙirji. A daddafe na sha farfesun, na haɗa da tea. Magungunan ciwon jiki ta ɓaɓɓallo mun na watsasu. Cikin ikon Allah sai bacci ya ɗaukeni. Bani na farka ba sai da duhu ya rufa, dana miƙe tsaye sai naji da dama inji mutan nijar suka ce da dama. Alwala na ɗauro a ƙaramin toilet dake cikin ɗakin. Raak'a ɗaya na iyayi a tsaye, dana yi ruku'u kasa ɗagowa nayi sai zarcewa sujuda nayi, sabida ji nake dana tankwara bayan wani ƙashin ka iya ɓallewa in shiga uku. GWADABE MARAƊI Da daddare sosai Gwadabe ya shiga gida. Dan Hadiza ma ta ƙaraci jiranshi, da sunturin zuwa ɓarayinsu harta haƙura ta kwanta. "Kaine da daddare haka Gwadabe, ai daka raba tafiyar biyu." Cewar Auwala dake karɓama Gwadabe jakarshi. Sai da ya zauna daɓas a ƙasa yace. "Kai dai bari. Allah ya iso damu lafiya. Da fatan na sameku lafiya?" A tare suka waiwaya inda Mammada ke bacci yanata gwarti. Dariya suka saki su biyun. "Wannan matarshi ta shiga uku da wannan gwarti nashi" Cewar Auwala yana dariya. Gwadabe yace. "Kai kuma taka matar ta shiga uku da shegen cin abinci ba" Harararshi Auwala yayi. "Au to taka matar dame ta shiga uku, ko kai goma kake ba tara ba?" Dariya ya saka yace. "Ga gajarta ga tumbi" Dariya suka saka. Gwadabe dai ya miƙe ya samu ya watsa ruwa yazo ya rama sallolinshi. "Ga abinci Hadiza ta ajjiye maka. Tazo shashennan yayi sau talatin, gorin matan malam ne yasa ta haƙura, sai ta kawo abincin na ajjiye maka. Ammanfa tare zamu ci ato" Kai Gwadabe ya girgiza kawai. Ya jawo tiran silvern da kwanakin silven ke kai. Kwano na farko dafa dukan shinkafar manja ce da bushasshen kifi. Ɗayan ƙaramin kwanon kuma farfesun kazar Hausa ne, sai zoɓo cikin kofi me murfi na silver. Tunda ya buɗe abincin yaji yana wani irin ƙamshin spices na musamman. Da ya saka a bakinshi ji yayi tunda yake bai taɓa cin abinci mai daɗi da ƙamshin wannan ba. Yaci abincinnan da yawa, ragowar Auwala ya janye kwanon dan dole. "Auwala Hadiza ce tayi wannan girkin amman?" Saida ya yagi naman kaza kana yace. "Itace. Hadiza ba baya ba wajen iya dahuwa, damma bakaci miyar tuwonta ba. Lokacin da take gidan tsohon mijinta ina yawan kai mata ziyara kasanni da son sanwa" Kai Gwadabe ya gyaɗa yace. "Amman mijinta ya tabka babbar asara daya saketa." "Inji wa? Ko kai Hadiza tayi ma irin abinda tayi a gidan mijinta sakine zai tabbata a garete. Kai bata da daɗi fa wajen kishi. Kishinta na hauka ne. Kai dai kabi a hankali. Kuma Allah ne ya jarabceta shi yasa ma ta faɗo hannunka a lokacin da kai kuma tuni ka amshi soyayyar wata. Wallahi ba ƙaramin so Hadiza take yi maka ba da har ta amince da kishiya tun kafin aure ma" Gwadabe yayi shiru yana jinjina lamarin, tare da auna maganganun Auwala a ma'aunin hankali. Tsoronshi Allah tsoronshi tashin hankalin da zaije ya taɓa zumuncinsu. Kuma gashi ya kasance namiji mai son walwala da dauwakammen farin ciki a gidanshi. Amman yaci alwashin yin bakin ƙoƙarinshi na ganin bai kunna kishin Hadiza ba a cikin zamantakwar tasu. Yanata tunanin irin zaman da zaiyi dasu su biyun. Da waɗannan tunanin gari ya waye haske ya maye gurbin duhu. Nan samarin gidan suka soma layin yin wanka domin fita nema. Masu goge baki nayi, masu goge takalmi nayi. Gwadabe yana zaune a dakali yana jiran fitowar su Auwala. Sai ga Hadiza ta ratso hannunta rike da babban tire. Ƙurama takunta kallo Gwadabe yayi. A tsanake take yin komanta babu bankaure balle hayaniya. Saida ta kusan zuwa inda yake sai ya miƙe ya karɓeta Sadiƙu ya ja tsaki yace. "Aikin banza harara a duhu" Da Hadiza da Gwadabe duk suka waigo suka dubi Sadiƙu dake shirin ficewa a shashen. "Allah ya shirya. Barka da isowa Dijena" Murmushi tayi kawai ta dubeshi tace. "Ya hanya, ya ka baro kowa da kowa?" Fitowar Auwala ce ta katse amsar da Gwadabe yaso yaba Hadiza. Tiran kayan karin ya karɓe. "Ina kwana Yaya?" Hadiza ta faɗa tana haɗiye dariyarta. "Hadiza lafiya. Gwadabe zo da hanzari mu karya mu fice aikine damu sosai" "To Dijena kije, in muka dawo saimu samu mu tattauna, in kuma baki tsarabarki. Amman naji daɗin yin tozali dake, kuma na yaba da abincin da kika girka mun" Farin ciki fal zuchiyar Hadiza tace. "To godiya nake yi. Nima yanzu wajen aiki zan tafi, in ka dawo ma tattauna ƙila bakasan ina fita aiki ba. Sai kun dawo Allah ya tsare" Juyawa tayi ta kama hanya. Gwadabe kuma ya shiga ciki, suka gama karyawa tsab, aka fita nema. Basu suka dawo ba sai bayan isha yau sunyi dare. Suna dawowa Mammada yayi wanka ya tafi zance. Auwala kuma ya shiga cikin gida ya karɓo musu abincinsu. Bayan sun gama ci, Gwadabe yayi wanka sai ya tura yaro yai mishi kiran Hadiza. Bata fi minti goma ba sai gata. Yana hangota ya miƙe tsaye. "Yau dai muje waje mu ɗan zazzaga muna tafe muna zanca Uwar gida sarautar mata" Gwadabe shi ya soma fita Hadiza tabi bayanshi, sai da suka fita waje ne suka jera. "Soma bani labari. Da safe kince zaki tafi aiki. Dama kina zuwa aikine bansani ba?" Murmushi tayi "Na fahimci abun ya tsaya maka. Dan in ba haka ba ba hirar daya kamata mu soma ba kenan. Amman tunda ita ka zaɓa Shikenan zaka ji. Dama tun ina gidan tsohon mijina ni madam ce ( malamar makaranta) Ina koyar da yara ƴan primary school, fannin arabiya, nike ɗaukarsu Qur'ani da wasu littattafai biyu. to bayan aurena ya mutu ne, sai malam yaje da kanshi ya nemi alfarmar a bani hutu in kammala iddata. To ranar monday na ci gaba da koyarwa. Kaji abinda kake son ji" Kai ya jinjina yace. "Ashe tare da Madam nake ban sani ba? Kinga in mu kai Aure zaki dinga koyar dani karatu in sha Allah. Yayi kyau ni bazan hanaki aikinki ba, dan Shafa ma tana aiki a Najeriya, kuma wanta ya roƙeni akan in akayi auren zata nemi aiki anan inta samu to." Lokaci ɗaya annurin dake kan fuskar Hadiza ya gushe. Shiru ya biyo baya, sai tafiya suke yi a hankali. Hardai shi Gwadabe ya kawar da shirun ta hanyar jefo mata tambaya" "Yaushe su Malam zasu dawo ne?" A taƙaice ta bashi amsar. "Babu wanda yasan ranar dawowar tasu" Shiru ya ƙara biyo baya, wani ɗan dakali Gwadabe ya gani sai ya dubi Hadiza yace. "Zauna ki huta sarauniyar mata, takawarki Lafiya. Kinsan bana son ki wahala" Dole dai sai da ya dawo mata da farin cikinta, ta hanyar furta mata kalamai. Zama tayi tana dariya. "To Hadiza nima inaso zuwa gobe in soma sana'ar dafa magunguna na gargajiya. Wanda ya shafi na basir, maganin rana, da shawara, zan dinga ajjiyewa a wajen aikinmu. Sai ki taya ni da adda'a, in Allah ya taimakemu sai kika sana'ar ta karɓeni" Sun jima suna taɓa hira, daga bisani kuma suka koma gida, shi yayi shashensu, itama tayi nasu shashen. Kwana Gwadabe huɗu da dawowa, Baba Fhatsima suka dawo suma da daddare. A washe gari Malam ya tattare kan iyalinshi harda na gidan auren. Bayan Baba Fhatsima ta rarrabawa kowa tsabarshi, Malam ya soma magana. "Maƙasudin wannan taron dai shine zaman lafiya da haɗin kai. Ni da kaina na roƙeku da ku daure ku haɗe kawunanku, ko dan haɗin kan ƴaƴanku. A ko da yaushe a cikin fargaba da damuwar rashin haɗin kan iyalaina nake kwana in tashi, lamarin da ya kusan haifarmun da ciwon zicciya. To a wannan karon duk macen data nuna taurin kai, ko ta hana yaran ɗakinta yin biyayya a kan dokikina to magana domin Allah zan sallameta. A yanzu in ganku kayukanku a haɗe shine babban abinda ke gabana." Take aka shiga ƙusƙus a falon. Malam yayi shiru yana kallonsu kafin ya ci gaba da cewa. "Doka ta farko shine, dole ko wanne yaro a cikin gidannan da safe yabi ɗakunan matana kab ya gaishesu wajibine wannan, duk wanda ya saɓa zai gamu da abinda baiyi zato ba balle tsammani. Kuma tun yanzu inaso yarana in cakuɗesu a ɗaki ba kamar yanzu da suke a wawware ba. Ina nufin Mammada zai koma Ɗakin su Sadiƙu, shi Sadiƙu ya koma gadon Mammada, Sabitu kuma ya koma cikin su Zailani, shi zailani ya koma ɗakin su Safiyanu. Haka dai nakeso ya canja, domin su soma sabawa da juna tun kafin su yi aure. Sannan a yarana kab, da matan nawa duk me son wani abu daga gareni ga Tasi'u na ɗaura mishi duk nauyin. Wanda yasa girman kai sai ya haƙura. Shine magajina, Babban wa uba, dole a bashi matsayinshi" Baba asshi ce ta miƙe tare da cewa. "Malam inada..." "Dakata Asshi. Wannan ba malam ɗin da kika sani a shekara talatin baya bane. Ki zauna ban ba kowa izinin magana ba, asalima bana buƙatar maganar kowa. Duk matar da taji ba zata iya bin dokikin gidana ba, ƙofata a buɗe take" Jin irin yadda Malam yake faɗa sai kowa ya shiga taitayinshi. Malam ya dinga tsaro yanda yakeso ayi. Abinda ya kamata ace tun sanda yara suna ƙanana ya kamata ayi, shi malam sai yanzu akeyi. Kuma wannan ya farune a bisa yanda Malam ya kasa zama tsayayye a gidanshi. Ya sake ko wacce mace inta shiga da irin abinda take shigowa dashi. Shi kuma ya kasa taka burki a gidan nashi. A haka gidan ya cika da yara, a lokacin da yaran suke ƙanƙana babu irin rikicin da ba'ayi a gidan. Uwargidan Malam ce kaɗai mace mai haƙuri da kawaici. Itake ke iya kawar da kanta in matan malam nayi ma yaranta hukunci, kuma mafi akasarin hukuncin na son zuchiyane. Babu irin hawala da makircin da Baba Fhatsima bata gani ba a wajen Baba Asshi ba. Dan har takai ta kawo malam ko ƙofar ɗakinta baya iya kallo in ba ranar kwananta bane. Ta baza mulki tayi abinda takeso. Sai da malam ya sake auro mace ne Baba Fhatsima ta samu sassauci a gidan, domin kishi an kasafta gida biyu a lokacin. Malam kuma duk matar daya auro saita kasance itace ta gaban goshi a wajenshi, harma baya iya ɓoyewa, hatta cefanan ranar girkinta dabanne kawai. Ire_iren waɗannan halayyar ta maza ta rushe haɗin kai da zaman lafiyar haula da dama. MRS BUKHARI *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* Domin neman ƙarin bayani 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BOOK 2 BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 10 Haka sabuwar rayuwar gidan Malam taci gaba da kasancewa. Yaran basu da wani zaɓi face su bi umarnin mahaifinsu. Yayin da daga bayan fage iyayensu mata ke musu huɗubar tsiya, tare da cusa musu tsanar Baba Fhatsima da yaran ɗakinta. Ko gaishe da Baba Fhatsima suka je yi, cikin wulaƙanci da rashin girma suke gaisheta. Itako Baba asshi ko kallon inda Baba Fhatsima take bata yi, ƴar gaisuwarma sun dena, domin tunaninta shine Baba Fhatsima ta murɗa kambunta ta sake ƙwace gida a karo na biyu. Dan in ranar kwananta ne Malam ya dinga sunturi kenan a tsakar gidan. Itama in kwananta ne, zata shige turaka ta nitsu ta yi gyara na musamman a kunna turaren wuta. Da yamma taci adonta da kaya masu tsada tayi tafiyarta turaka. Wannan sauyi na Malam da Baba Fhatsima ya tsayama matan gidan daram a zuchiyarsu. Yayin da wasu suka soma sake sabon salon kula da malam, su Baba Asshi kuma bata da aiki sai ya da habaici a tsakar gida. Kuma taci alwashin ba zata taɓa tambayar Tasi'u kuɗi ko yai mata wani abun ba. Itama tana Ɗa Jamilu, kuma dai dai gwargwado shima yana samu, saidai Allah yayi shi da shegiyar rowa, dan ko matarshi Siyama da ƙyar take ɓamɓararshi. Tasi'u ya dage sai gini aketa faman yi, abunka da kuɗi gininnan bai jima ba aka kasheshi, har an soma buga rabta. Ta wani ɓangare harya gama siyen kayan gado, da kujerun ƙannenshi mata, sauran tarkacen kitchen iyayensu mata ne zasu yi musu. Ya kuma riga ya sallami Baba Fhatsima da ishasshen kuɗin kayan kitchen ɗin Hadiza, da kuɗaɗen gudanar da harkar sha'anin bikin al'ada. A ranar da yaba Baba Fhatsima kuɗinne tace. "Su matan Babanka ka basu kuɗin da zasu gabatar da sha'anin bikin al'adar ne, kasan fa ana kashe kuɗi musamman ga su da zasu aurar da maza. Kuma jibi ma za'aje kan goron mazan gidan. Jibi kuma Malam zai tafi Takai yaje ya sanar musu da lokacin biki" Tasi'u yace da Baba Fhatsima. "Baba ban ba ko wacce daga cikin su ko sisi ba. Sabida a tunanina tunda auren maza zasu yi su yaran zasu bama iyayen kuɗin komai. Yarannan ba ganinki suke da gashi ba" "Hatta Malam basa ganinshi da gashi. Kai dai kai musu domin Allah domin kuma uwayenka ne. Hatta Amaryar malam nasan zata yi nata taron, da anko duk zata yi naga sai fitarwa akeyi kashi_kashi. Itama ka bata abinda zata yi hidimarta dashi. Allah yayi albarka" Shiru yayi can ya girgiza kai yace. "Babu komai za'ayi musu kamar yadda kika ce, in sha Allah. Naga yaronnan Gwadabe yayi ƙoƙari wajen haɗa akwatunan bikin. Sune can ko? Badi'a ta faɗamun yasa kaya masu tsada ba laifi, ta yi goshi a matsayinta na Bazawara " Baba Fhatsima tayi dariya. "Yayi ƙoƙari babu shakka, Allah ya fiddamu kunya. Dan Allah ya buɗe musu kwanakin baya sosai. Kaga zinarin da suka tono yana da nauyi ainun. Shi ya taimaki harsu Auwala suka ƙarashe haɗa akwatunan nasu. Kuma sana'ar magani da yake yi matan gidannan na dariya suna tsokanar Hadiza wai taci baya. Sana'ar na taimaka mishi, ana siyen magungunan nashi sosai. Naga har almajiran malam siye suke yi. Kaga akwatin kishiyar Hadizan ma, komai iri ɗaya ya zuba har kala. Shine ma take ta ƙorafi ƙasanta da rashin hankali. Da abokinshi ma ya ɗauke mishi akwatin ita waccan ɗin, da dai ya samu halin yine yace zaiyi abinshi" Jawo mishi akwatunan tayi gabanshi, komai na ciki bai bambanta ba, girman takalmi, ɗan kamfai, rigar Mama shine kawai na ɗaya ya zarce na ɗaya. Dariya Yaya Tasi'u yayi. "Hadiza daru ba. To na ƙara mata ko kala biyar ne" Baba Fhatsima tayi dariya itama tace. "Rabu da'ita. Ta haɗa kaya famtimoti Babba, kuma duk ta ɗinka abinta. Ga malam yayi musu kayan fitar biki. Ai kasanta da kishi, kullum cikin faɗa nake mata. Jibi Babarku Altine tana hanya zata zo ita da Balaraba ƴar wajenta. Kuma inajin sai an gama bikinnan zasu koma." Altine ƙanwa take ga Baba Fhatsima. Mace mai kirki da son zumunci. Sai dai ba'a wanyewa lafiya tsakaninta da matan malam. Dan bata barin ko ta kwana. Balaraba kuma ɗiyarta ce, wacce da akaso ayi musu haɗin gida da Tasi'u. Amman a lokacin Tasi'u ya riga ya soma soyayya da matarshi Badi'a. Sai Balaraba ta auri saurayinta dama tana da saurayinta iyayene suka so ayi haɗin gida kawai. Yanzu kuma Allah yayi ma mijin nata rasuwa ya barta da yara bakwai. "Allah sarki. Mama altine jibi ana hanya? To a ɓarayina zasu sauka gaskiya wannan karon ƙwaceta zanyi." Haka dai akaita hidimar biki ta ko wanne ɓangare, gidan a kacame yake ko da yaushe. Washe Gari akaje kan goron Samarin gidan tare da kai fantimoti. An tsayar da biki wata biyu cib. Ranar a gidan ba'ai girki ba, abincinan da aka tawo dashi daga kan goro ya isa har maƙota sunci shi a wadace Washe gari Malam da Jamilu suka kama hanyar Takai a motar Jamilun, tare da akwatin Shafa wanda daga nan za'a kai nan gidansu Shafa dake Takai ɗin. TAKAI TA KAWO TA SABA DA SAUKAR BAƘI Babala tana zaune a tsakar gida, ta jiyo yaran gida na yima Baba Magaji sannu da zuwa. Sai taga akwatuna Bara'u na shigowa dasu. "Kai Bara'u waɗannan famtimotan fa shi Yaya Magaji shine ya tawo dasu?" Murmushi Bara'u yayi yace. "E dashi suka tawo. Kinganshi ma ya shigo" Yana kaiwa nan ya fice. Yaya Halima da Goggo Iyatu suka fito daga ɗaki riƙe da haɓa har Yaya Magaji da Jamilu suka ƙaraso. "Maraba lale da zuwa, Jamilu yau kaine a cikin gidannan iko sai Allah. Wasa gaske Gwadabe naso ya dawo da tsohon zumunci" Cewar Babala data haɗe ranta tayi kicin_kicin. "Baba ku shigo daga ciki, kunsha hanya, ga magriba tayi." Cewar Yaya Halima kenan. "A'a Uwata bamu ruwa a buta kinji magriba ake kira, in muka yo Sallah mazo a tattauna a tsanake. Hambali bai ƙaraso bane, na kirashi shi da Harisu nace duk mu haɗu anan." Goggo Iyatu tace. "Yanzu fitarsu masallaci kuka iso" Ruwa aka basu a buta su kai alwala tare da tafiya masallaci. Tare suka dawo dasu Yaya Hambali. Abinci aka dire musu. Baba Magaji da ya kai loma bakinshi bayan an gaggaisa sai ya soma jawabi. "Wannan fantimotin auren Gwadabe ne, da Shafa ƙanwar abokinshi Tamu, ƴaƴan mirgayi Hamisun Dogo. Da daddarennan nake son za'a kai kayan tare da sadaki baki ɗaya. Wannan dalilinne yasa nace Hambali da Harisu su tawo dan su jagoranci komai tunda sune manya." "Kaga ni Yaya ban gane me kake nufi ba. Au jita_jitar da muke ta ji a gari akan Shafa Gwadabe zai aura ashe da gaskene itan zai aura. Ina batun Hadiza ƴar Fhatsima?" "Du su biyun zai aura kuma rana ɗaya da izinin Allah " Dariya Yaya Hambali ya saka. "Ikon Allah waina kwance ya faɗi. In banda talaka da nemo wa kai jarfa ina Gwadabe ina mata har biyu Baba. A duba lamarinnan fa, kar a siyar da akuya ta dawo tana cin danga. Dan Gwadabe ba mai ƙashin ma arziki bane shi tun fil azal, duk abinda yaronnan ya taɓa sai ya lalace. Yanda Allah yaimun wannan sutura bana jin zan iya shiga wata hidimar Gwadabe, ko dan gudun kar jarfar dake bibiyarshi ta shafeni." Jim Baba Magaji yayi, yana kallon Yaya Hambali da maɗaukakin mamaki. Yaya Harisu yace. "Ni kaina bazan iya saka hannu a duk wata hidimar Gwadabe ba. Yaron dake tafiya da bakin uwa" Jamilu ya buɗe bakinshi dan mamaki. Goggo Iyatu kuwa sai sharar hawaye take yi. "Ohh Yaya Laila ce dai baka ƙaunar Gwadabe ya aura. Amman gashi ka jona mishi ƴarka kai. Yarinyata ta ƙi zaman aure, yanzu haka tana gida an sake sakota, bayan mijin yayi mata kafirin duka." "Hmmm ni kam nama rasa ta cewa wallahi. Yaya Gwadabe kaima ɗanka ne. Kai kaɗai gayyane zaka iya zartar da komai. Gidansu Shafa ka sani. Allah ya sanya alkairi shine kaɗai abinda zance. Amman Gwadabe ai ya nuna mun bai haifu a cikina ba. Tunda ni ina matsayin uwarshi sai dai in ji ƙishin_ƙishin a gari zai auri ƙanwar abokinshi. Yaranshi duk ya tattare ya damƙa mishi. Gashi da ƴan uwa ya nuna baya ƙaunarsu. Damme zasu ƙaunaceshi shim... "Ya isa haka nace" Baba Magaji ya dakatar da Babala da kakkausar murya. "Lallai Babala ba zaki taɓa yin hankaliba har abada. Ke da kanki kike farraƙa kan yaranki. Shin me Gwadabe yayi miki ne a rayuwa haka. Ba dai akan Auren beyerabiya bane? To naga ya rabu da'ita. Na ɗauka ƙiyayyar zata tsaya a iya nan ki sama yaronnan albarka ko zai ga haske. Me yasa kika zame mishi baƙar uwa? To Shikenan ni zan tsaya mishi ayi komai. Ku kuma" Ya nuna su Yaya Hambali yace. "Kubi duniya a hankali. Ita dukiya baƙuwace. Kuma wanda Allah yace sai yayi arziki sai yayi. Ina jiye muku ranar da zaku kasa haɗa idanu da Gwadabe, ko kuma ranar da zaku kasa matsowa inda yake sakamakon ɗaukakar da zai samu. Jamilu ci abinci ka kinkimar mun famtimotinnan muje kai da Bara'u ku rakani na ishi Gwadabe uwa da uba. Ƴan uwanshi na can sun share mai hawayenshi, suna sonshi, kuma suna zumuncinsu. Akwai ranar ƙin dillanci. Yaya Halima ta buɗe baki zatai magana, Baba Magaji ya dakatar da'ita ta hanyar ɗaga mata hannunshi. Matan gida suka shiga tururuwar zuwa gaishe da Baba Magaji, daurewa yayi ya dinga fara'a dan kawar musu da tunani. "Gida naga yasha gyara, waye yayi muku gyara haka" "Ka ganshi ɗan albarka wanda tun yana tsumman goyo yake samun tabarraki. Allah yayi mishi lifiɗi yayi gamdakatar da arzikinshi. Kuma ya ja ƴan uwan nashi a jiki anata harkar arziki. Nanda wata biyar ma umara zamu dani dashi da matar tashi." Babala ce take magana da fara'a sai dariya take yi. Baba Magaji yace. "Madallah Allah yaima dukiya albarka Hambali. Jamilu muje ko?" Tashi Jamilu yayi ya soma jan famtimotan zuwa waje. Yana jaye dasu Baba Magaji yana biye dashi a baya. A ƙofar gida suka tarar da Bara'u duk suka rankaya. Sun samu tarba ta mutunci gaya. Nan suka gabatar da sadaki da kayan aure. "To nan da wata biyu dai muke so a ayi komai a gama. A duba, sabida tare muke son ayi komai a gama yarane kusan goma za'ayi bikin nasu tare" Ƙannen mahaifinsu Shafa ɗaya daga ciki yace. "Allah ya nuna mana lokacin. Yaro yayi mana bayanin komai. Mu dama mun daɗe a shirye. Fatanmu Allah ya kai rayuwarmu" Nan su kai sallama da juna. Ta ɓangaren Babala daren ranar kasa bacci tayi, ta saƙa wancan ta kunce wancan. Babu irin abinda bata hasaso a ranta ba dangane da irin abinda Baba Magaji yayi mata. Abun ya matuƙar ɓata ranta har kuma taci alwashin ba zata taɓa taka ƙafarta da sunan zuwa bikin Gwadabe ba. Kuma ƙafarta ba zata taka dan matanshi sun haihu ba. Kuma taci alwashin duk ranar da ya tako ƙafarshi yazo inda take sai tayi mishi tijara. Da waɗannan ire iren tunanin garinta ya waye. Ta ɓangaren Baba Magaji ma, sai tunani yake yi, tare da jinjina halayya irin ta Babala Haka ta taso tun asali da wata iriyar baƙar zuchiya mai shegen riƙo da rashin yafiya. Uwa uba ga jahilci da zaman karkara dake ɗawainiya da rayuwarta, in banda haka taya uwa zata dinga adawa da gaba da duk ci gaban ɗan data tsugunna ta haifa, akan dalilin da ba dalili ba. Ko washe gari kafin Baba Magaji ya tafi sai da ya sille Babala tas, itama kuma ta fusata dashi, dama a wuya take dashi nan tayi tsalle ta dire tace. "Magaji dakata kaji, ba zaka zo har gidan mijina ka nemi tozartani a gaban ƴaƴana ba. Sabida haka kar ka sake tako ƙafarka kazo inda nake, ka soma gyara gidanka tukunna, ka dena rashin adalci a tsakankanin matanka tukunna kafin kazo mun da guntun wa'azinka. In aka sake faɗamun wani abu daya danganci Gwadabe ma Allah ya'isa ban yafe ba. Ka faɗa mishi matsawar ya tako Takai da zummar zuwa ganina nonona da yasha sai ya biyani. Haka in ya tako ƙafarshi yaje wajen ƴan uwanshi Allah ya isa ban yafe mishi ba ehe, kaje ka riƙeshi" Idanu Baba Magaji ya runtse. Yaya Hambali kuwa ya saki wata siririn murmushi, Yaya Harisu kuwa fuskarshi kadaran kadaham. Matan ƙannen mijin Babala nan suka shiga bata haƙuri tare da nuna mata rashin kyautawarta akan furucinta, gudun kar ta sake ɓalɓanta rayuwar Gwadabe da ci gabanshi. Amman suma sai ta dira a kansu. Baba Magaji yace. "Ki rubuta ki ajjiye, daga Gwadabe har ni ba zaki sake saka kowa a idanunki ba. Jahilar kawai tur dake a matsayin uwa ga Gwadabe. Ki sani wata rana zaki shiga jerin masu layin son yin tozali da Gwadabe." Yana kaiwa nan ya ja hannun Jamilu rai a ɓace yana share hawayenshi. Itama ta shige ɗaki fuu su Yaya Hambali suka mara mata baya. "Wallahi ina shirin taka mishi birki kenan kika tanka Babala. Akan mitsiyaci Gwadabe za a shigo har fadarki ai miki ɗiban albarka. Anya Baba Magaji yana ƙaunarku kuwa?" Cewar Yaya Hambali " "Inafa yake ƙaunata. Ai Shikenan babu kare bin damo, yaje gashi ga Gwadaben, shima bai iya gyara gidanshi ba, ya kasa haɗe kan matanshi sai gidan wasu zai shigo ya gyara" Baba Magaji" Yana zaune a bayan mota, sai tunanin irin furucin Babala na rashin albarka yake yi. Abu biyu sune suka tsaya mishi. Na farko cire Gwadabe daga cikin ahalinta. Na biyu kiranshi da tayi ba adaliba wannan ya taɓashi, hakan yasa ya sake ɗambar ganin kan gidanshi ya haɗu, duk da shi kanshi ya sani abune mai kamar wuya" Basu suka isa Maraɗi ba sai wajajen goman dare. Da sallama suka shiga gidan, matan gidan sai hada hadarsu suke yi a tsakar gidan, ko wacce kaji muryarta ta to da yaranta take hirarta. Sannu da zuwa suka yi mishi, rannan nashi a mugun murtuke ya wuce ɓarayinshi. Yana wanka Baba Fhatsima ta shigo, yana jin shige da ficenta, ɗaure da babban tawul ya fito. Idanu ya zuba mata tayi kwalliyarta sai wani dattijuwar kyau take yi. Ajjiyar zuchiya ya sauke, Fhatsima tana daga cikin matan da kallonsu ke kawar da damuwa, gami da mantar da ɗa namiji inda ya dosa. "Maraba da dawowa ranka shi daɗe babban malamina" Zama yayi a kusa da'ita. "Barka Fhatsima da fatan na sameku lafiya? Na yi ma Allah godiya daya kasance lura dani a cikin wannan daren yana hannunki, ƙila da sai dai a wayo gari zuchiyata ta buga. Dan kece kaɗai mai iya mallakata" Farin ciki ne ya lulluɓe illahirin jikin Baba Fhatsima. Abinci ta zuba mishi suka dawo falo. Yana ci tana mishi taɗi ananne ta sanar dashi zuwan Altine ƙaunarta da da Balaraba "Allah sarki Altine uwar zumunci yanzu harta zo dan ayi komai tare da'ita. Yaya mijin nata da surukanta?" "Suna lafiya dukkansu. Ina ruwan Altine daru, ko ɗazu sai da su kai ƴar hayaniya da sahibarka Asshi" Murmushi yayo yana ƙoƙarin karantar yanayinta. Kishinta na mallakar kai yana burgeshi, tana da tsantsar kishi, amman kishin da bai rufe mata idanun da zata cuta ma abokan zamanta ba daidai da kalma. Kishin da bai gusar mata da nutsuwa da kamalarta ba. Yanzu ambaton ashshi kawai da tayi, sai da hancinta ya ɗanyi wani doro, wanda da wannan doron hancin Malam ke gane tana yanayi na kishi. Ɗauke tunanin nata yayi ta hanyar cewa. "Hmm kinsan yanda muka kwashe da shashashar yarinyarnan kuwa?" A nutse ta kalleshi tace" "Da naso ne ka nutsu tukunna ko zuwa da safe saimu tattauna, domin sake maimaita maganar a cikin yanayin fishi ka iya haifar da wani fushin." Da wannan Baba Fhatsima ta rinjayi mijinta. Ta ɓangaren angwaye kuma sun sake zage damtsen neman na tuwo, biki sai ƙaratowa yake yi gida yayi kace kace. Gwadabe bai san halin da ake ciki ba, domin Baba Fhatsima ta ba Malam shawarar ya rufe zancan har sai zuwa bayan biki sai yai mishi bayani a tsanake. Gidan Amare yayi shar dashi ya ɗauki fenti gabaki ɗaya harda cikin gidan malam. Yara kuma sun gwangwaje iyayensu da gyaran daƙuna suma dai sun zama amare a wajen Malam. Malam da kanshi ya tusa angwayennan gaba ko wanne ya zaɓi ɗakinshi duk zubinsu iri ɗayaa ne babu wani bambanci, Gwadabe dakunan matanshi suna jere, a kusa da ɗakin Sadiƙu, kafin ɗakin Gwadabe kuma ɗakin Auwala ne. Key Malam ya miƙama ko wanne. Su Tasi'u da Jamilu su zubin ɗakunansu yafi yalwa, kuma ɗakuna uku ne a ciki kasancewar suna da yara maza da mata. Malam ya basu umarnin ana biki saura sati guda su dawo wannan ɓarayin amare su shigo su samesu a ciki. Haka dai akaita shidimar biki. Ana saura sati guda ɗaurin aure baƙin nesa suka soma cika gida. Su Anty Badi'a kuma suka ƙaura izuwa sabon gida. Nan malam kuma yasa aka fente dakunan da suka tashi wanda Tasi'u ya fita yace Baba Fhatsima ta koma ciki. Wanda jamilu ya fita kuma yaba Baba Asshi. Nan Suwaiba da Amaryar malam suka shiga tashin hankali da tunane tunane dan su a tunaninsu tunda dai su da sauran mammora a jikinsu su ya dace ace Malam yaba waɗannan ɗakuna ba matanshi tsofaffi ba. Ta bangaren Amaren gidan malam su su huɗu sai gyaran jiki aketa faman yi musu. Magunguna kuwa a dama musu wannan da madara, wannan a dama da Nono haka dai aketa faman yi musu. Hadiza dai tunda baƙi suka cika gidan nasu bata saka gogan nata a idanunta ba, wayarma ba kasafai suka fiye yinta ba. Ita dai sai tsuma kanta take yi, burinta ta zama sarauniyar zuchiyar Gwadabe. Kuma kasancewarta bazawara harda yara yasa tafi ƴan matan kannenta shirya kanta. Ƙawarta Hassana itace take ta bata dabaru da sirrin zama da kishiya, sakamakon ita a gidanta itace ta uku. Hadiza ta ɗaura ɗamarar yaƙi da jahilin kishi, ta ɗaura ɗamarar bama Gwadabe farin ciki, da kiyaye dukkannin ɓacin ranshi. Amaryarshi kuma tsakaninsu gaisuwane, dan bata jin zata wani iya zaman hira ko wani sakin fuska da kishiya. Kowacce dai ta iya allon ta ta wanke. Kasancewarta Amaryar ƴar gida har an mata jerenta tsab, ta samu kaya fiye da aurenta na fari, ɗakinta yayi matuƙar kyau. Tun kafin gida ya cika da mutane Baba Fhatsima da Goggo Altine su ka zaunar da Hafiza sukaita karanta mata karatu masu amfani ( gaba cikin labarin zamu ji me suka faɗa mata a aikace a gidan Gwadabe) Duk abinda suka faɗa mata tayi ram dasu a ƙwaƙwalwarta sai jujjuyasu take tana farin ciki. Harma Allah _Allah take a soma wasan. Rana bata ƙarya Allah ya kawo mu ranar biki. Tun ranar Monday aka soma shagulgulan da suka shafi al'adu, ta ɓangare Amare da angwaye. Ta bangaren ƴan Takai. Goggo Iyatu, da Goggo Rahila Matar ƙanin Babansu Gwadabe ne a manya suka tawo. A yaran mata Laila tazo, sai Abuwa matar Ɗan Goggo Hajiyayye matar Ƙanin mahaifin su gwadabe, ita tsufa ya kamata Abuwa ke wakiltarta zuwa duk wani sha'ani na dole. Babala dai dasu Yaya Hambali da matansu ko ƙeyarsu babu. Gida ya kacame da sha'ani. Mayu da ɓarayi sun samu abun nema, kowa sai farauta Laila kuwa duk abinda taga anyi wasarere dashi saita adanashi, ta sake ta shiga jami'a sosai. Duk wanda yai wasarere da jakarshi, akwai Laila da ire_irenta da yawa a gidan biki su zasu adanama mutum kayanshi hausawa sukace mai son abinka ya fika dabara. Amare sai kyau suke sha, su saka wannan sutura su canja. Hadiza tayi kyau fiye da aurenta na fari, domin yanzu tafi sanin kanta fiye da baya, a baya akwai ƙuruciya. Amman a yanzu tasan cikakkiyar darajarta ta ɗiya mace. GWADABE: Ranar da aka ɗaura aurensu Hadiza da safe, Gwadabe nata shirin kama hanyar Najeriya shi da Baba Magaji. Sai ga Auwala ya shigo ɗaki ya sameshi sun sha uban ankon farar shadda mai maiƙo. "Ango mijin Hadiza. Malam ne yace in yi kiranka zaku yi magana" Murmushi yayi mishi yace. "Ango mijin Zakiya bada kan ka a sare kaje gida kace ya faɗi" Dariya suka saka dukkansu. Hularshi ya ɗakko yasa suka fita tare. Ratsa mata ƴan biki sukayi, sai nunasu akeyi gwanin sha'awa duk kaya iri guda suka saka harda su Yaya Tasi'u. A zaure suka samu Malam da aminanshi dattijai biyu. "Gwadabe tafiyarmu Najeriya an fasa. Yanzu haka maganar da nake maka an ɗaura auren naka acan Tamu da Bara'u su suka tsaya akan komai, yanzu aka ɗaura auren. Sun kirani suna hanyar tawowa da Amarya, motar kaya kuma tun jiya da rana ta kamo hanya. Babu mamaki zuwa rana ka gansu. Na sanar ma Fhatsima Dangin amarya da masu jere suna hanya. To sai ka zauna a cikin shirin tarbar amaryarka" Murmushi Gwadabe yayi, kanshi na ƙasa sai godiya yake yi ma Malam kawai, domin bashi da bakin gode mishi, yayi mishi komai a rayuwa. Sallamarsu Malam yayi suka fice waje wajen abokansu. Hadiza: Ta bangaren Hadiza tunda Malam ya sanar ma Baba Fhatsima Amaryar Gwadabe suna hanya. Sai cikinta ya ɗuri ruwa, har wani zazzaɓi taji yana shirin sakko mata. Goggo Altine ta dubi Baba Fhatsima tace. "Zuwa bayan la'asar sai a shigar da ita gidanta tunda itace uwar gida, yana da kyau Amarya tazo ta sameta a ɗakinta. Dan haka bari in fita in sanarma da su Hadizan Zendar." Wani sanyi Hadiza taji ya kwaranyi daga kanta zuwa ƙirjinta. Kafin azahar masu jere suka iso motar jere daban, motar iyaye daban. Sun samu tarba ta arziki an taresu da kaji da farfesu, da tuwon ɓula ( tuwon ruwa) Ana idar da sallar La'asar aka fito da Amarya Hadiza. A zaure suka yi kaciɓus da Malam yana tsaye yana jiran fitowar tasu. Tsugunnawa Hadiza tayi tana hawaye a gaban Malam. "To Hadiza ina fatan wannan fitar da zaki yi daga gidanku yasa fitace ta har abada sai dai zuwan daɗi in sha Allah MRS BUKHARI Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 11 Ga wannan a rage zafi zuwa monday zan dawo ka'in da na'in 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. "Na horeki da haƙuri da kawaici. Kiyi zaman aure irin wanda mahaifiyarki take yi. Sannan kiyi kishi irin nata Hadiza. Allah yayi albarka Allah yasa sai dai a fitar da gawarki. Ga wannan ɗan kunnen zinarin ki adanashi zai miki Amfani, ko da zaki siyar ki tabbatar juya kuɗin zaki yi ba wasa dasu ba. Altine ku tafi da'ita" Altine ta ɗaga Hadiza suka fita aka kaita ɗakinta. Barinta akayi ita da ƙawayenta sunata hirarsu. Ƴan uwan Shafa kuma sai jere suke yi mata dan a gaskiya Shafa tafi Hadiza kaya musamman kayan ƙawa na ɗaki, dangin samiru da kwalla. Kuma sai da aka mata bango guda na kwalliyar tasa, sai ɗaukar idanu suke yi. Duk labari ya isarma Hadiza, sai taji babu daɗi domin ba hakan taso ba. Ƴan kuɗaɗen data samu na gudunmawa ta ɗungume ta ba Aminiyarta suka ƙaro mata kumbula da kwalla. Kafin magriba har sun dawo, suka kuma sherawa, tare da sake ma ɗakin fasalin daya dace. Ta bangaren angwaye ana fitowa sallar magriba ko wanne ya jaye abokanshi suka nufi cikin gida domin gabatar da WATSI. Inda ake ma ango watsin alawa, da kuɗi. Ana samun kuɗaɗe sosai. Ko wanne ango dangin mahaifiyarshi ne suka shimfiɗa musu taburmai. Akaita watsin kuɗi da cingam. A wannan rana angwayen sun samu kuɗi na mamaki domin wannan ranar tana daga cikin ranakun nuna bajintar dangi, da amfanin tarin dangi. Su Gwadabe sun samu kuɗi sosai a wannan rana dan dangin Baba Fhatsima masu kuɗi rabinsu da kwata suke Aure, uwa uba ga Yaya Tasi'u shima ya nuna bajintarshi, da yarsu Zarah. Wankan kudi kawai akaita musu, lokaci ɗaya kallo ya dawo wajensu Gwadabe. Mata sai ihu da guɗa suke yi. Dangin Baba Fhatsima sukaita musu ɓarin kuɗi kawai. Kiran sallar isha ne ya dakatar da abun. Nan suka kwashe kuɗaɗensu a buhu suka yi gaba. Nan kuma aka shiga kawo amare ɗakunansu, tare da bataliyar ƙawayen Amare. Da misalin sha ɗayan dare gungun motocin ƴan kawo Amarya suka iso ayari guda. Bus biyu, da karamar mota biyu, ƙaramar mota ɗaya ta amarya da ƙawayenta ce, ɗayar ƙaramar motar ta abokan Gwadabe ce, Bus ɗinnan kuma yaran mata da tsofaffi, da yara ƙananu ne aka kwasosu, kunsan dai yanda ƴan ƙauye suke tafiya raɓaɓe _raɓaɓe da bataliyar yara. Cikin gida aka shiga da iyaye tsofaffi, da yaran mata. Ƙawayen Amarya da amarya kuma aka barsu a ɗakin amaya. Su Bara'u kuma suna waje sun haɗe cikin samarin maraɗi sai shan gahawa da gashasshen nama suke yi. Kofar gidan malam kamar rana tsabaragen taron maza abokan angwaye, kowa ya haɗa dabarshi da abokanshi. Ga almajiran malam sai daudalar cin tuwo suke yi anata nishaɗi. Cikin gidanma haya_haya duk inda ka kutsa. Duk an zube a tsakar gida sabida yanayi na zafi ga tarin jama'a. Ƴan Takai sun samu tarba da abinci lafiyayye da soyayyun ƴaƴan shila harda lemun limca, da 7up. Ƙawayen Amarya nama da shayi aka tarbesu dashi, sai bireɗensu suke yi. A tsakankanin Amare Takwas da suka tare a ɗakunan mazajensu. Ko wacce an zuba mata kaya wannan na wane wannan, ga gara ta ban mamaki da akayo musu, ko wacce ɗan ƙaramin kitchen ɗinta cike da kayan masarufi, wasu harda miyoyin kaji aka haɗosu, wasu kuma dambun nama. Ko wacce Amarya tana a tsakankanin ƙawayenta sunata farin ciki. Saɓanin Hadiza da Shafa da zuchiyarsu take cike da zulumi gami da fargabar haɗuwa da juna. Ko wacce a zuchiyarta tana fatan tafi ƴar uwarta ko da da abu ɗaya ne ta fannin halitta. Hadiza tafi Shafa shiga cikin damuwa dan ita hakan ya taɓa mata annurinta, sai tayi laƙwam ta yi tagumi tana kallon ƙawayenta zaurawa da matan auren da suka nace sai sun tayata kwanan ɗakin miji. Su kuwa sai dariya da bada labarin kishiyoyi, da irin makirce_makircen wasu matan suke yi. Ta bangaren Shafa kuma ita tsoronta ɗaya ne kawai, yanda take ji da ganin budewar idanun zaurawa da ilimin zaman aure da suka fi ƴan mata dashi, shine tsoronta, dan ta fahimci tamkar Gwadabe yafi bata lokacinshi fiye da ita. Amman da tamai ƙotafi sai ya nunar mata ba hakan bane yanayin aikine kawai ke hanashi kiranta a waya. Da Waɗannan tunane_ tunane dare ya tsala. Maza a ƙozar gida suka kwana. Ƙawayen Amarya da zafi yayi zafi a tsakar gida suka kwana abinsu. Washe gari aka tashi da buɗar kai kenan. Tun sassafe Amare sukaita kacaniyar wanka, ƙawayen Amarya kuma ko wacce da abinda take yi dai. Cikin gida: Kukan yara da hayaniyar mata kawai kake ji. Amaryar Malam da Baba Asshi suna daga gefe suna gulma. "Malam ya sakar mata kuɗi sai wadaƙa take yi dasu. Da anyi magana Malam yace ɗanta ne mai kuɗin gidan. Kinga wata sarƙar zinare da ta saka jiya kuwa, kuma bata sa ko ɗaya daga kayan da akayi mana na fitar biki ba. Shaddoji take ta sakawa masu tsada." Cewar Baba Asshi wacce takai wuya tun sanda aka soma biki, da irin abincinnan da dangin Baba Fhatsima sukaita dafawa na alfarma dan basa ko cin abincin bikin, nasu abincin suke girkawa daban. Da kuma irin kayan ɗakin da Tasi'u yaima Hadiza ba irin na sauran yaran ba, dan hatta gara na Hadiza yafi yawa. Ga watsi da kuɗi da su Baba Fhatsima sukaita ma su Auwala, ga irin suturu da Baba Fhatsima take ta ketawa. Waɗannan abubbuwa sune suka haɗi suka tsaya ma matan Malam. Yaran gidan sai gulmar abubbuwa suke taima iyayensu mata, su kuma sai tauna lamarin suke, suna dagon maganganu masu nauyi da suke shirin fesarma Malam in an gama bikin. Baba Fhatsima: Tana tsaye cikin farar shadda da ɗan kunnen azurfa, da Ƙannenta suke maganar abinda ya dace a dafa ma baƙi. Altine tace. "Ga farfesun naman rago sukutum tun asubar fari Lamiso ta ɗaura. Wanda za a shigar ɓarayin Amare baki ɗaya. Sai ruwan shayi da burodi inaga ya isa haka. Ni batun abincin buɗar kaima zanyi miki Yaya. Anan ɓangaren naki ne za ayi yau dai biki zai ƙare?" Baba Fhatsima tace. "Yauwa Altine kinyi kyan kai, dama na fison a basu lafiyayyen kayan kari. Dangane da abincin buɗar kai matar wannan yaron Badi'a komai yana hannunta ita zata yi, abincine nasu na yaran zamani zata yi dake ba mai yawa bane, Amare kaɗai za a ɗibarma sai ƴan uwana dake ɓarayina, sai abokan Malam. Goggo Mairo tace. "Amman Yaya tun jiya Asshi take takalarmu da faɗa, sai ni nake ta daddanne Altine akan kada ta sake tayi magana. Yaron Saminu ɗazu suna alwala a ƙofar ɗakinta tana fitowa ta shiga ƙunduma musu ashariyar da duk wanda yaji yasan da iyayen yaran take yi ba dai waɗannan kuca _kucan yaran ba." Baba Fhatsima tace. "In banda ke da abinci Mairo. Ai Asshi ba zata canja ba, mai hali baya taɓa fasa halinshi. Ku dai ku yi watsin ruwan tsarki dasu, maza a tabbatar an sallami baƙi kowa ya samu Abinci. Ke Altine ki dubo mana kwanan Amare" Baba Fhatsima tana gama faɗar haka ta wuce turakar Malam. Goggo Altine ta nufi ɓarayin Amare ta dubo lafiyarau. Ko wacce tana tare da danginta, Amare anci ado, ko wacce tubarkalla kyakkyawa da'ita gwanin sha'awa. Haka dai aka gwangwaji buɗar kai, akaci aka sha harda kiɗan ƙwarya a tsakankanin matan. Zuwa bayan Isha taro ya watse gida ya rage daga baƙi sai ƴan gida. Gwadabe. Ta ɓangaren Angwaye kuma tun da suka idar da sallar isha Malam yace su sameshi a turakarshi yanason tattauna muhimmin zance dasu. Hakan kuwa akayi, suna idarwa suka je suka samu Malam a turakarshi tare da matanshi duka. Ko wanne ya nemi waje ya zauna a gefen uwarshi, abokansu kuma suka wakiltasu dan siyo tsarabar amare. "Toh Alhamdulillah an yi taro lafiya an watse lafiya, banda ƴan kunji_kunji na mata wanda ya zame musu al'ada. Ni abinda yasa na taraku a gaban iyayenku domin su zame mun shaida shine. A cikinku duk wanda ya nemi fitina ko tada tarzoma a cikin wannan gidan naku, haƙiƙatan zai fuskanci hukunci mai tsanani. Ya zame muku dole ku so junanku domin da hakanne matayenku zasu haɗe kawunansu ayi zaman lafiya. Matsawar matayenku suka fahimnci a tsakaninku ƙiyayya da rashin jituwane. To suma fa ba zasu taɓa haɗe kawunansu ba. In kuma basu haɗe kawunansu su ba, to haka zaku hayayyafa yaranku su taso babu jituwa a tsakaninsu, kamar yadda iyayenku su ka yi. Domin sune ummul aba'isin ɓata komai. So nake in gyara gidana dan gudun barin baya da ƙurar da in ta tashi ba a san adadin mutanan da zata tule musu idanu ba. Ku zaunar da matayenku ku fahimtar dasu mahimmancin ƴan uwansu. Ku umarcesu da zaunawa da kowa Lafiya. Tasi'u da Jamilu sun isheku a matsayin uwa da uba. Duk abinda ya taso ku sanar musu, zasu maganceshi sai in yafi ƙarfinsu sai mu ji a cikin gidan. Ina fatan kun fahimceni, kun gane inda nasa gaba ko?" Sabitu ne ya kalli Hannafi Wanshi, suka taɓe bakinsu carab a kan idanun Baba Fhatsima. Baba Asshi da Amaryar Malam da suka samu haɗewar kai a bikinnan suma suka wani ɓata fuskarsu. Itako Suwaiba sai kallon Malam take yi bakinta cike da abu faɗe. "Fhatsima kece Babba da akwai abinda zaki ce ma yaran naki a gurguje?" Buɗar bakin Suwaiba ta katse Malam ta hanyar cewa. "Ai daka barsu Malam sun tafi abokansu suna jiransu, karfe kusan tara saura ai ya kamata su tafi ga iyalinsu. Duk abinda zamu ce ai mun riga mun faɗa musu tun ba yanzu ba. Ko ba gaskiya ba, Asshi, Amaryar Malam?" Ta tambayi su Baba Asshi da suka ji daɗin katse Malam da Suwaiba tayi. Su Gwadabe kuwa sai sunkiyar da kansu suka yi ƙasa dan yanda tayi maganar ba daidai bane ace tayi ma Malam a gaban yaranshi ba, domin Malam ya haifi waɗanda suka girme mata nesa ba kusa ba. Itako Amaryar Malam tace. "Sosai kuwa Suwaiba. Ai duk wani huɗuba mun riga da mun yima yaranmu Malam. Itama Fhatsima tayi ma yaranta a ɗaki, sai nake ganin ba dole bane sai ta haɗesu duka an ƙara ɓata musu lokaci ba." Auwala da yake jin kamar dama ya kashe Amaryar Malam ya ɗago yana mata wani irin muzurai na ɓacin rai. Baba Fhatsima ce ta dubeshi ta tausheshi da idanunta, dan ta fahimci matan Malam ransu a ɓace yake da Malam ne akan ɗinkewarsu da tafiyarsu umara. Malam kamar ruwa ya cinyeshi haka yayi tsit. Ji yake kamar ƙasa ta tsage ya shige dan tsantsar kunyar da matanshi suka bashi a gaban yaran nashi. Da ƙyar da siɗin goshi ya yaƙi zuchiyarshi ya dubi Baba Fhatsima a karo na barkate. "Me zaki ce Fhatsima ko kuwa kin basu izinin tafiyar kema?" Ganin ɓacin rai maɗaukaki a fuskarshi da muryarshi yasa tace. "Abinda zan ɗaura muku akan abinda Malam ya faɗa daya ne. Kuyi ƙoƙarin ginin fondisho me kyau ga iyalinku dan gudun dana sanin data kasance ƙyayya maras amfani. Sannan ku sani hannu ɗaya baya ɗaukar jinka. Zanso ku kasance tsintsiya ɗaya. Banda tuna baya, gani ga wane akace ya ishi wane tsoron Allah. Ku je Allah yayi muku Albarka " Da Ameen su Gwadabe suka amsa, bacin su sauran yaran babu wanda yace uffan. Fuu suka fice, iyayen nasu suna a mugun fusace suka miƙe. Malam: "Ku dawo ku zauna ban sallameku ba" Malam ya faɗa da muryar da babu wanda yasan cewa shine mallakinta. Duk sai da suka tsorata da irin yanda Malam yake zurga_zurga a filin falon. Duk suna tsaye harda Baba Fhatsima wacce ta miƙe yanzu. Sarautar Allah suka zubama idanu. Malam baice komai ba, bashi da niyyar cewa uffan, sai kai mari da gwauro yake yi. Cikin ɗaga murya gami da tsawa_tsawa ya soma Magana. "Ashe rainin da ku kai mun ya kai ku mun diban albarka a gaban ƴaƴana? Ashe rashin ɗaukata ba a bakin komai da kuke yi ba ya kai haka? Ashe ni bazan faɗa ku ji ba? Kaiconka Magaji da son ƙyale ƙyale yasa ka auroma diyoyinka iyaye maras tarbiyya. Allah na tuba ka yafe mun kura kuraina ya Allah. Suwaiba dake da Maman Inusa ( Amaryar malam) kuje gidan iyayenku har sai na nemeku" Kalmar data girgiza hanta da huhun matan Malam. Da sauri Baba Fhatsima tace." "Kar kayi haka Malam. In hankali ya gushe hankali ake turawa ya nemoshi. Me yasa zaka sallamesu alhalin gidan cike yake da jama'ar biki, ɗakunansu ma a cike yake da dangi na nesa. Kaima Allah ka yi haƙuri" Malam ya dubeta yace" "Ki barsu su tafi Fhatsima. Bazan laminci rashin ɗa a ga ko wacce mace a cikin gidannan ba. A tunaninsu damar da suka samu a baya zasu sameta yanzu ne? Ina ba wannan magajin da suka sani bane" Su Suwaiba dai jikin tatsaure yayi la'asar. Abun kunya ne ace yanda ta aurar da yara, yau a wayi gari wai malam ya korata gida. Itako Amaryar Malam kab danginta sun san itace tauraruwar gidan malam, yau sai ace a gabansu Malam yace ta tafi gida wannan abun kunya dame yayi kama?" "Malam kaima Allah ka barsu su zauna a ɗakinsu" Cewar Baba Fhatsima. Baba Asshi tama rasa ta cewa kallon Baba Fhatsima kawai take yi. "Shikenan sun shiga rigar alfarmarki Fhatsima. Ku fuce ku bani waje. Ammanfa ku sani ana watsewa a gidannan. Kuma ku tattare yanaku_yanaku ku ficemun a gida, har sai zuwa lokacin dana ga dama nace ku dawo" Jikkunansu duk a mace suka fice ko tari an rasa wacce zata yi. "Malam ka sassauta ma kanka dan Allah. Kayi haƙuri abi komai a sannu, in sha Allah gidanka zai gyaru ya zama kamar ko wanne gidan dake da tsayayyen uba. Ni dai a kullum ina sake jaddada maka ka zama mai magana ɗaya tak. Rarrabe magana itace ta soma kawo rabewar kai a gidanka, ka zauna kayi tunanin yanda zaka tanƙwara matanka. Korarsu bazai zama ya kawo gyara ba, sai sake rura wutar gaba da ƙiyayya." Da sauri ya katseta da cewa ."amman aya zata ji tsoro tunda taga an taune tsakuwa ma. Fhatsima abinda ya faru a baya kuskurene, a lokacin idanuna duk sun rufe bana ji baba gani, giyar ƙuruciya da lafiya na ruɗata. Dube ni a yanzu da ƙuruciya da ƙarfin nawa ya ƙare kuma na kasance cikin damuwa da hawan jinin da ni na saima kaina domin bazan ga laifin Asshi ko Suwaiba ba, sabida ni nace ina sonsu har suka amince mun. Kije ki kwanta babu damuwa, Nagode sosai Allah yai miki albarka. Ina mai daɗa baki haƙuri a bisa kuntata miki da nayi a baya, ruɗin sheɗanne" Ɗan murmushi tayi mishi tace. "Da an taɓo maza sai kaji suna cewa ai ruɗin shaiɗanne, alhalin son zuchiya ke rufe muku idanunku, sai kun shiga matsala ku zama abun tausayi. Allah ya kyauta sai da safe" Ficewarta tayi ranta ya sosu ainun. Malam ya fama mata daɗaɗɗen mikin daya jima yana cin ƙasan zuchiyarta tsawon shekaru. Ta ga rayuwa ta shanye takaici kishiya da ɗa namiji samfur_samfur, sai da ta kasance fiye da mugiya dan baƙin jini a wajen kishiyoyi. Hawayenta taa share daidai isowarta bakin ƙofarta. Baba Asshi ta ja tsaki tace. "Fhatsima dani kike zancan ni dake shege ka fasa. Asirinki akan iya Malam zai tsaya dama shi shanyayye ne. Amman ni Asshi naci dubu wallahi sai dai ceto" Ɗan guntun murmushi Baba Fhatsima tayi. Ta tattako izuwa kusa daf da Baba Asshi. "Asshi kenan. La haula maganin mai tsafi, nasha tabara na sha yasin. Ni Fhatsima a tarbiyyar da iyayena suka bani babu zuwa wajen boka. Da biyayya ake kwace miji, ba da boka ba. Na riga nayi tasiri a rayuwar Malam tasirin da babu wata mace data isa ta kamo rabin matsayina. Ai matar fari daban take, darajarta ta musamman ce" Tana kaiwa ƙarshe ta juya ta shige ɗaki ta bar Baba Asshi cike da tunani tare da zabarin zuwan wayewar gari, domin ungulu na son komawa gidanta na tsamiya, dan tana tunanin Baba Fhatsima zata rushe mata shirin da tai ta shiryashi sama da shekaru talatin. Gwadabe: A gurjuge suna fitowa kowa ya koma cikin tawagar abokanshi. Gwadabe kuwa daga Tamu sai Bara'u ne a gefe da gefenshi. A jejjere kusan dukka suka shiga cikin gidan. Ƴan Takai dangin Amarya da su Laila suna tsakar gida suna cin tuwo sai kwasar hira akeyi. Idanu Laila ta zuba ma Gwadabe har gobe da jibi tana son Gwadabe, kuma duk da mata biyu daya aura lokaci guda baisa ta karaya ba, tana ji komai daren daɗewa haƙonta zai cimma ruwa. Gadararta tafi matan Gwadabe kyau da hasken fata sosai. Sai dai ta mance halayya da tarbiyya sune abun ado a wajen ko wanne ɗa ba kyan sura da haiba ba. "Angwaye masha Allah jibeku a jere gwanin sha'awa" Cewar Duduwa tanayi tana Dariya " Bara'u ne ya kulata suka ɗan tsokani junansu haka dai sama_ sama. Ayashe tace. "Ku shige abinku kunji" Wucewa suka yi izuwa ɗakin Hadiza, domin ta kanta za a soma itace uwar gida. Shafa ɗakinta ma cike yake dam da ƙawayenta. Da sallama suka shiga falon Amarya dake buga ƙamshin turaren wutan halut oud, da kuma ƙamshin sabon fenti da sababbin kaya. Hasana ce ta nuna musu waje a saman kujeru suka zauna. "Mun same ku lafiya, ya akaji da taro?" Suka haɗe baki wajen amsawa. Bayan haka ƴar nasiha ce ta biyo baya daga bakin Tamu da Bara'u taƙaitacciya. Nera dubu ukun Najeriya suka basu a matsayin kuɗin sallamar ƙawaye. Bara'u ya ajjiye ledar kazar da kayan shayin, su ka fita tare da ƙawayen Amarya baki ɗaya. Gwadabe dai bai yi yinƙurin rakiya ba ma. Komawa yayi da hanzari kusa da matarshi Hadiza. Ɗagowa tayi suka haɗa idani ta sakar mishi murmushi mai taushin gaske. "Barka da zuwa angona, yau dai ga Hadiza a matsayin taka kuma uwar gida a gidanka" Murmushi yayi, a lokaci guda yanayinshi ya ɗan sauya. Ƴar yarbawarshi yake tunowa da lokacin da aka rakashi ɗakinta, da daren farkonsu, da irin farin ciki da jarumtar da Iyabo ta nuna mishi. Idanu ya lumshe a hankali. "Lafiya kuwa sai naga yanayinka ya sauya. Wani abunne?" Hadiza ta tambaya a ɗan tsorace. Jin muryarta cike da damuwa yasa ya ture tunanin komai. "Babu komai Uwar gida. Wannan daren namu ne mu angwayen gidannan mai albarka. Yanzu dai mu soma da yin nafila bisa sunna, sai mu baje in ciyar dake kazar amarci. Ke kuma ki shigar dani duniyar sama jannati" Dariya tayi mishi kawai. Shi ya soma tafiya ban ɗakiin yayi alwala kafin itama ta shiga tayo nata. Yanda tsarin bayan gidan gidan yake shine, da farko in ka buɗe ƙofar farko, ɗan wani wajene kamar ƙaramin falo, kitchen da ban ɗakin suna kallon juna, sai ƙofar shiga falon tana tsakiyarsa. Ginin wajen rabi ne, kana iya ganin shigar mutum banɗaki da fitowarshi, ɗan ginine rabi, da ƙaramar ƙofa. Haka duk tsarin ginin yake. Siminti ne luwai_luwai a dandamalin kitchen da banɗakin, da ƴan ƙofofin katako dai haka. Gwadabe ya ja su Sallah raka'a biyu, tare da adda'ar samun zaman lafiya, zuriya dayyiba. Daga nan suka ɗan taɓa ciye_ciyen kaji da madarar shanu. Gaga_gaga Gwadabe ya soma raba Hadiza da kunyarta, cikin salon dabara da hikima Gwadabe ya samu nishaɗi da farin ciki da nutsuwa a wannan dare mai albarka. Masoyan suka cakuɗe suka zama abu guda, zukata suka cika da sabon shauƙin juna. Cikin wannan shauƙi bacci yai awon gaba dasu izuwa kiran sallar assalatu. A mugun gajiye tulus Hadiza ta tashi zaune, doguwar rigarta ta hango a wancakale kusa da sib, jawo rigar tayi da ƙafarta ta zura kafin ta miƙe. Ashe Gwadabe idanunshi biyu ita yake kallo, har ta sa kai zata fita yace. "Ina zaki je?" Juyowa tayi tana kallonshi magashiyan a kwance, hasken lantarki na haske shi. "Dama zan kunna risho ne in ɗuma mana ruwan zafi" Miƙewa yayi tsaye. Tayi saurin kawar da kanta, abinda ya ankarar dashi kenan. Sai ya suturta kanshi ta hanyar gajeren wando. "Basshi da zafinnan zai fi kyau in watsa na sanyi. Sai dai in kece kike buƙatar ruwan zafij ko? Ya ɗan kashe mata idanu" A tsaye ya wuce ya barta tana murmushi. Bayan gida ya shigeta kuma ta shige kitchen. Tana jiyo ɓuruntu a ragowar kitchen ɗin Amaren gidan. Ɗakin Sabitu dake kallon nasu ma, ta hango shigar Sabitu bayi, buɗe ƙofar falon da yayi ne hasken lantarki yasa ta hangoshi. A gurguje Gwadabe ya fito. Kayanshi ya mayar ya fice masallaci kasancewar bai ɗakko boron kayanshi ba. Fitarshi Hadiza itama tayo wankanta a gurguje ta shige ɗaki. Duk yadda taso kar a ganta sai da Sabitu da Matarshi suka ganta. Sallar asuba ta gabatar bacci sai ɗebeta yake yi. Murmushi tayi sanda ta tuno abubbuwan da suka wakana a daren jiya. Wata sabuwar rayuwa a jiyan Gwadabe ya shigar da'ita. Yau ne ta tantance tsakanin namiji da mata maza. Dan tsohon mijinta irin ƴan ƙauyannanne da basu iya tura ƴan aike kafin zuwansu ga iyalansu ba. Salamatu kwanta kawai ta sani ita, domin dashi aka raineta. Amman yau taji daɗi da garɗin da ƙawayenta ke yawan bata labari. ( Khadija maidoki)Sib ɗinta ta buɗe ta ciro wata gorar magani, data ɗaga kai sai da ta sha rabi kafin ta mayar. Tana mayarwa Gwadabe yayo sallama ya shigo fuskarshi yalwace da fara'a da ƙyallin man angwanci raɗau a fuskarshi. Kusa da'ita ya ƙarasa ya riƙe hannayenta duka biyu. Baice mata komai ba sai kallo da yake ƙare mata. Haƙoranta biyu da suke ɗan fitowa waje yake kallo. Shi a idanunshi ba matsala bane, sai dai a idanun mutane. Tsarin zubin fuskarta ya ɓoye wannan nakasun haƙoran nata. MRS BUKHARI Ce [06/08, 9:35 am] BADI'AT IBRAHIM: *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 [15/08, 8:00 am] BADI'AT IBRAHIM: Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 ZEE MUSA COLLECTION 💃🏼💃🏼 Tana siyarda atamfofi da laces da shaddar da sauran kayan Yara da shoes and bags da material zee Musa collection ba, anan ta tsaya ba tana siyarda kayan kitchen da supplement da saurankayayakin masu inganci kaidai ka garzaya 🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️Kar ayi Babu Kai ko ka tuntibeta ta wannan number din kamar📞📞08029882667 nagodee 💃🏼💃🏼💃🏼 NAMA YA DAHU..... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI GAWURTATTU UKU 12 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. Number na dana saka a jikin littafi ya sake tono mun masoyana masu son magana dani sosai. Daga ranar dana saka numberna izuwa yanzu wlh bazan iya ƙirga adadin saƙonnin dana riske ba. Babu abinda zance da masoya sai godiya. Hakan ya sake fallasa ƴan bati suma, son so 😀👍🏻 IYABO: Ina kan sallaya hannu da kaina a sama ina roƙon Allah ya kawo mun sanadin komawata ƙasata najeriya kar in mutu a wulaƙance a inda rayuwata bata da amfani. Yaya Hamma na tuno da ƙoƙarin da yayi akaina domin in haƙura da tafiyar naƙi. Haka zalika Burodami Debisi yayi ƙoƙarin hanani tafiyarnan idanuna sun bushe gani nake tafiyar itace mafita. Ashe rabon shan wahala ne, ko da wannan ciwon bayan aka barni ai na horu. Fati ce ta shigo ita da Sima ɗan daudun ƙawarta. waya take yi sai larabci take yi, wasu zantukan ina fahimtar me take cewa wasu kuma bana ganewa. Na fahimci da namiji take magana, kuma maganar haɗuwa suke yi. Data ajjiye wayar sai na dubeeta nace. Faty na lura kamar mu,amala da maza shine sana'arki ko?" Na ƙura mata idanu ina karantar yanayinta. Sima ya tafa hannaye yace. "Yau ni naga jar jaraba ido da ido, Iyabo kike ko wa?" Ni dai ban tanka shi ba. Ido cikin ido tace Faty tace." "Ƙwarai da aniya. Jikina shine jarine, babu kasuwanci mai ci a ƙasarnan sama da wannan. Kema kuma dama ce da zaki tara kuɗaɗen da ko kin koma Najeriya ba kiy babu talauci. Kin ganni ina da gidajen da ake mun haya. Mijin da zan aura dawowata kawai yake jira. Na tuttura dilolin kayayyaki gida Najeriya dana koma nima na zama daga cikin waɗanda za a dama dani, hatta kayan kitchen ɗina da kayan ƙyale_ƙyalenmu na mata duk nayi ma kaina. Hmmm Iyabo nima da wanke_wanken na soma. So uku ina zubar da ciki a wannan ƙasa, na farko yaron gidan aikinane yai mun ciki, na biyu Ya Babana ne yai mun ciki ( Ya Baba kamar uban gida ake nufi). Na ukun abokin yaron gidan aikina da yaro daga Canada yai mun ciki. Wuya babu irin wacce ban sha ba a gidan aiki. Wasu fa har rasa rayukansu suke yi. Kema in baki haƙura da gidan aiki ba, wallahi sai aikin gidan larabawa ya nakasa miki jiki, baga irinta nan ba, ciwon baya ya soma kama ki ba, duk da ciwon bayannan suke komawa najeriya su zamema danginsu layabiliti. Tun kafin ki rasa lafiyar ƙafafu a mayar dake Najeriya hajaran majaran ba lafiya ki zame musu nauyi, ke baki tara kuɗi ba, su ki cinye musu nasu gara ki haƙura da wannan aikin." Wani zumm naji a jikina tamkar an jona mun shokin wallahi. A dibibice nace. Duk a gidan aikin kika haɗu da wannan ƙaddarar? Amman Faty me yasa baki koma Najeriya ba? Wannan rayuwar ai ba mai ɓullewa bace, babu yadda za ayi ka saɓi Allah kuma kaga haske a gaba. Ni dai da in bi maza gara in koma Najeriya a nakashe, ke koma in mutu, sai dai ai mun da ƙarfin tsiya. Kema ina mai baki shawarar ki tuba, daga ke har Sima" Hawayene ya zubo a idanunta sai girgiza kai take yi. Sima kuwa dariya da wata girgiza yayi ya bude jakarshi ya zaro hanbaki mai ruwan toka ya sake shafawa. Kullum bakinshi da wannan janbaki kamar akuya ta dumbuji gari. Faty ce kawai tace. "Ni zanfita sai gobe zan dawo. Ƙila in na dawo in tsokata miki kaɗan daga cikin rayuwata. Zaki fahimci neman kuɗi ya wajaba a gareni. Karki mance ina binki kuɗin abinci. Akwai laban da cake in zaki ci gasu can" Ta nuna mun inda cake ɗin yake da bakinta ta fuce abunta Sima na biye da'ita. Ajjiyar zuchiya kawai na sauke, haka na kwana ina tubka da warwarar tunani, hankalina tuni ya daɗe da komawa gida. Sai kuma inna tuno da irin rayuwar da Dadana take yi a gidan azzalumin mijinta sai inji na ɗan samu ƙwarin guiwar zama in nemi kuɗi da GUMIN HALAL ( BATUL MAMMAN) In na tuno baƙar azabar aikin gidan larabawa da furucin ire irensu Faty sai inji zuchiyata ma ta tsinke. Washe gari da safe sai ga Hajiya ta leƙo dakin. Wani kallon wulaƙanci ta watso mun. "Ina dai fatan ba kin dawo bane da zummar kinbar gidan aikin ki ba ko? Dan ƴan gidan aikin ki sun kira suna tambayar yaushe zaki dawo. A tsorace nace da'ita. Bani da lafiya ne shi yasa na dawo. Da zaran jikina ya warware zan koma kan aikina" "Ya dai fi miki. Me yake damunki da baki iya zuwa mun gaisa ba?" Na kwashe labarin yadda nake ji na bata. Abun mamaki sai ta kwashe da dariya harda buga ƙafarta. Lokaci guda kuma sai ta saki tsaki tare da cewa. "Aikin banza. Da wai me kuka ɗauka, da kun shigo ƙasar kun zama masu arziki ko me? Hatta karuwan cikin gidannan da kike ji da gani suna shan wuya. Ki tambayi tantiriyar ƴar barikin data baki mafaka zata baki labarin da yadda ta soma. Ko da yake ƙila nemanki take yi ko shi yasa ma ta ajjiyeki" Tana gama faɗar haka ta saki labulen ɗakin ta barni ina shurɓune majina. Da ƙyar na miƙe a daddafe na gyara ɗakin, bayan naci kukana na ƙoshi na gode ma Allah. Baya da ƙafafu sun matsa mun, ban ɗaki na shiga na ɗan gargasa jikina da tawul, na shafe jikina tas da man zafi. Sai na ɗan bibbi bango na fita domin in samar ma cikina ɗan abun da zanci. Fitata ke da wuya, sai ga wata ƴar matashiyar budurwar da ba zata haura shekaru goma sha bakwai, sha takwas ba. Idanunta a kumbure bakinta da hancinta sai jini da majina da yawu ke dalala. Faɗi take. "Ku taimakeni bana gani. Mutuwa zanyi. Na roƙe ku ku mayar dani ƙasata najeriya na gaji da wannan azabar." Yib sai ta runtuma a ƙasa take sai ba numfashi. Hankalinmu ya tashi ainun duk muka rufu a kanta masu kuka nayi, masu salati nayi, masu cewa a kira gidansu a sanar musu halin da take suna yi. Ni dai ruwa na nemo na sheƙa mata sai ta sauke ajjiyar zuchiya ashe suma tayi. Tiri_tiri kuma suka jata zuwa ɗakinta dai. Yarinyarnan ashe gidan da take aikine, mijin matar ke kwanciya da'ita shine matar ta kamasu cikin dare. Shine tai mata irin wannan kafirin dukan. Ita ko Hajiya dawa Allah ya haɗata bayan mu. Ashe duk haya_hayar da muke yi tana. Ɗakinta bacci take yi. Tana tashi ta dira a wuyanmu ta inda ta tsikara ba tanan take ja ba. Duk mu kai tsit kowacce tayi tsamo_tsamo. Muna cikin haka yara da manyan da suka mayar da kansu fasiƙai dan cimma buri, huɗu daga cikin waɗanda suka fita kwanan gida suka shigo, ciki harda Faty da Sima. Shigowarsu ce yasa Hajiya ta sarara mana. Abinci na siya tuwo miyar kuka mai tsadar gaske. Komai fa akwai na gida najeriya takari ke siya, akwai maza da mata takari sosai, to su suke sayen wannan abinci. Su kansu masu abincinnan Hajiyoyin kansu ne in suka dawo gida Najeriya. Ina zaune ina cin tuwona, na dulmiya tunanin ko a wanne hali Dada take oho. Sai naji maganar Faty. Ɗagowa nayi ina lashe hannuna ina kallonta du a lokaci guda " "Nace zan ɗan tsokata miki labarina. Amman a dunƙule zan baki" Ajjiyar zuchiya na sauke nannauya. Ina jinki Faty. Nace da'ita tare da bata hankalina baki ɗaya. Tsulum Sima ya shige banɗaki da ɗaurin ƙirji yanata yauƙi. "Mahaifina mai auri saki ne. A iyakar tasowata matan da mahaifina ya aura sunfi ashirin. Yara a gidanmu kuwa kamar bakin masallacin juma'a. Rashin tasowarmu da iyayenmu Mata, sai ya gurɓata rayuwarmu musamman mu matan. Sai mu fita a lokacin da muke so. Ke in kwana bakwai zaki yi bakya gida babu mai tambayar dalili. Ba lalle ne ma a lura bakya nan ɗin ba. Yawo na dinga yi kwararo_kwararo domin samun na abinci da suturar arziki a matsayina na matashiya. Tun tasowata na riga na saba da kula da kaina a matsayina na mace, Babanmu iyakar abinci kaɗai yake iya bamu, shima sau biyu kuma marar daɗi. A shekara sau ɗaya rak yake mana sutura kala ɗaya rak. Ke zaki sai sabulun wanka dana wanki, ke zaki sai man shafawa, man goge baki, ke zaki biya kuɗin kitso, kayan kwalliya, turare. Ke komai da kika sani, ki faɗamun me zai sa ba zamu saba da kuɗi ba. Me yasa idanuwanmu ba zasu buɗe ba? Ita ko mahaifiyata tana can tana auren wani marar mutuncin yana mata gashin ƙuma. Itama bata samu kulawa ba, balle ta kula dani. Yaran data haifa acan ma a ƙarƙashinta suke ita ke ɗawainiya dasu har mijin ma. Kinji somi_somin taɓarɓarewar rayuwata. A wannan yawon ɓel_ ɓel Allah ya haɗani da wani ɗan shaye_shaye harda ƙaddarar aure da yaro ɗaya tilo. Kullum sai ya jibgeni babu ranar banza, matan banza har gadon sunnah ake shigomun dasu. Uƙuba muraratan. Ana cikin haka Allah da ikonshi sai ya sakeni akan karuwarshi, yace in musu girki ni kuma na dire nace banyi. Sai ya sake ni. Na tattare kayana na koma wannan rayuwa ta gidanmu, ko da aka ganni a gida babu wanda yace dani ƙala. Nima nayi banza da kowa. Gaga_gaga naita faɗi tashin neman na tuwo. Har sanadi yasa na tawo wannan ƙasa ta dalilin ƙawata. Labarin zamana a gidan Larabawa ban ɓoye miki komai ba. Naso in tuba in nutsu, amman abun yaci tura ni kuma idanuna ya bushe akan kuɗi da son ceto mahaifiyata da ƙannena da Babanmu ba ɗaya ba. Alhamdulillah yanzu su suna cikin farin ciki, kullum mahaifiyata a cikin sanyamun albarka take. Wannan shine zan iya baki a taƙaice." Girgiza kai nake ta yi, sai jujjuya labarin nake yi a ƙwaƙwalwata, ina mamakin uba irin na su Faty. Dada ce ta sake faɗi mun a raina. Amman in sha Allah da GUMIN HALAK zan kula da mahaifiyata da nawa ƙannen. Faty haƙiƙa kinga jalala." Ta ɗaya ɓangaren sai Gwadabe da yarana suka faɗo mun. Allah sarki yanzu nasan Gwadabe yayi aure, ko wanne irin hali yarana suke ciki oho. Nisawa nayi na ce. Haƙiƙa Faty kin taso a wata iriyar mummunar rayuwa. Ƙaddararki baƙar ƙaddarace. Amman fa babu wata hujja da zaki kafa domin ki saɓi Allah. Zina haramun ce, bai kamata ki kula da iyayenki da kuɗin zina ba" "Dakata Iyabo. Duk abinda kika gani a ɗakinnan, ko kika ci, hatta alfarma da nayi miki duk sanadiyyar kuɗin zinar ce. Kinga kema kuɗin yayi miki rana. Da yanzu daga ni har ke muna neman mafaka, tare da neman tudun dafawa. Jibeki fa jinyar wahala da azabar gidan Larabawa kike fama dashi. Kafin ke wasu sunyi, wasu fa tsabaragen wuya yankar jiki suke su faɗi su mutu, wasu su haɗiyi zuchiya." Da tsawa take yi mun magana yarinya ƙarama. Ko me ta tuna oho sai naji salama a muryar tata. "Iyabo tawa ƙaddararce haka. Kamar yadda ƙaddara ta zargo rayukanmu ta haɗamu a gidannan. Ki yi harkokin gabanki, ki barni inyi nawa Allah da kike ji da ganinshi me gafartama bayine." Hakane Faty Ubangiji Allah yasa mu dace. Ki taimaka ki ara mun wayarki zan kira gida. Tunda nazo ban samu damar ji daga garesu ba." Kamar dai ba zata bani ba dai. Sai ta miƙo mun. Number Burodami na lalubo a cikin kayana na kwafeta tsab a wayar na danna kore. Ruri biyu zuwa na ukun naji an ɗaga. Burodami Debisi Emi ni Iyabo ( Nice Iyabo) Ina faɗin haka sai kuka na baƙin ciki da nadama. "Ohh Ohh ohh Iyabo sai yau kika kira? Kin samu a damuwa musamman zuchiyar data shaƙu dake, ta horu da sonki. Ina fatan kina lafiya ko?" Sai kawai nace dashi. Lafiya lau, ya su Iyaa, da su Iyaa Beji da su Iya Kokodeen?" "Duk suna Lafiya. Jiya jiyannan Dada da Hamma suka koma. Sun zo kwanansu biyu. Dada ta damu da Iyaa ta faɗa mata baki kira ko sau ɗaya ba." Sababbin hawaye na matse a idanuna daɗin jin labarin Dada da Hammana ya sani cikin farin ciki. Allah sarki Dada. Suna lafiya ko? Kwanakin baya na ari waya na kiraka baka ɗaga bane. In Dada ta dawo a bata wannan lambar. Lambar yarinyar da muke ɗaki ɗaya ne. In akaci sa a na dawo hutu daga gidan aiki sai mu gaisa" Bai bani amsaba sai kuɗin ya ƙare. Kafin in ajjiye wayar sai ga kiranshi ya biyo ni. "To Iyabo zan bata. Ko bata zo ba zan shirya in an kwana biyu in kai mata. In naje gida zan kira in haɗaki da Iyaa. Kullum sai ta yi zancanki." Murmushi nayi nace. To Shikenan Burodami. Nagode, sannan a taya mu da adda'a. A faɗa ma Iyaa da Dada ina buƙatar adda'a" Buɗar bakinshi sai yace. "Masoyinki kuma mijinki na biyu ma zai hana idanunshi bacci wajen yi miki adda'a. Ina ɗan birri ɗan ƙauye me kiwo ba yamun ƙwacen masoyiya ba. In banda so da abinshi, me yasa zai kai kanshi dokar dajin da babu komai cikinta sai nono da fura" Ƙit sai na kashe wayarnan, raina ya ɓaci ainun. Miƙama Faty wayarta nayi, tare da yi mata godiya. Ban ɗaki ta shige, ni kuma naci gaba da cin tuwona. Sima na tsaye yana shafa mai yana rawa. Inata nazarin maganganun Burodami Debisi. Hammana ne ya faɗo mun a raina. Ya iyali ina son Hamma so marar abin misalin da hankali zai ɗauka. Dama zuchiyata wawuyar zuchiyace bata iya son abu ba sam. Haka kuma bata iya ƙin abu ba. Fitowar Faty daga banɗakine ya katsemun tunanina. "Da badan ƙafarki na ciwo ba, ai da kin rakani kasuwa inason sayen ɗan kunnen gold." Duk da nasan ina shan azaba sai nace mata. Da yaushe zaki je? Inason in ɗan fita ganin gari tsorone yake hanani dama." "Zuwa dare kinsan da daddare suke buɗe kantinansu. Khalifa zai zo ya kaimu. Daga nan ma sai ki rakani wajen wata ƙawata" Murmushi nayi mata nace da'ita. Tom Shikenan. Allah ya nuna mana sai in lallaɓa muje nima in gano gari kullum kana ƙunshe a gida" Yawu na haɗiye kana na ɗaura da faɗin . Ni ko Faty Uwani dai bata dawo daga gidan aiki ba tunda muka tafi ko?" Baki ta taɓe tace. "Ki yi tsammaninta dai zuwa shekara guda tim, ko wata shida haka. Kinsan fa su basu fiye son ana zuwa Ijaza ba. Ko mu sanda muke zuwa gidan aiki sai in mun gaji sai muyi ƙaryar ciwo shine zasu barmu mu tawo. Kinsan suna da tsoro gani zasu yi zaki mace musu ma" Dariya muka saka dukkanmu. "Allah kuwa. Haka suke da wannan tsoron. Mu kuma da munji aiki na shirin kashemu, sai mu langwaɓe" Haka mu kai ta taɓa hira. Daga baya kuma duk mu kai bacci, bayan mun yi sallar azahar kenan. Bamu muka tashi baccin ba sai kusan magriba. To ni daman a mugun gajiye nake, ga rashin samun wadataccen hutu. Wanka nayi a gurguje na ɗauro alwala. Faty ta faɗa banɗakin. Ina idar da la'asar ana kiran magriba. Tsakanin magriba zuwa isha a lokacin minti talatinne. Sai da mu ka yi isha Faty ta ajjiye mun wata baƙar abaya tace. "Ki saka wannan a saman kayanki. Ga turare sai ki shafa a jikinki" Karɓan turaren nayi a hannunta. Nayi kamar yadda tace. Ƙarfe taran dare Khalifa ya kirata yana ƙofar gida mu yake jira. Tare muka fito a jere mu uku. Nan naga dare tamkar rana. Kowa a cikin gida da ƙofar gidan sai hada hadarsu suke yi. Masu fita nayi, masu hira da takari nayi, gasu nan dai barkate. Wata baƙar mota me kyau muka shiga. Ina shiga na tarar da wani balarabe me gashi har kafaɗa, ya sa baƙar jallabiya yana ta kallona. Assalamu alaikum. Na furta murya na rawa. Dan naga kallon da yake yi mun yayi yawa. Faty ta juyo ta kalleni ta ɗan kashe mun idanu, ta maida kallonta wajen sima dake kusa dani tayi mishi murmushi. Na fahimci me take nufi sarai, tana nufin kar in ba da ita. Motarmu ta fice a layinmu a guje. " Masmuki ya bint?" Wanda muke gidan baya ya tambayeni da fara'arshi. Ismi Iyabo" Na furta a sanyaye. " Halta kafin? ( Tsoro kike ji)" Ya tambayeni, kafin in yi magana Faty tace. " Hiya daifun min najeriya" Sai ya girgiza kanshi yana mun dariya. " Anti jamilatun jiddan ( kina da kyau sosai) Halnastaɗi'u annakuna sahibain ( zamu iya zama abokai?). Ɗan dariyar yaƙe nayi dan a lokacin bansan me yake nufi da kalmar ba. Sima da murmushin ya bini. Sima kuma sai zungurata yake yi, nayi banza dashi. A bakin ƙaton kanti muka tsaya ko ina lantarki, sai hada_hada akeyi kamar rana. Ni dai ina biye da su Faty zungui_zungui. Wannan abokin saurayi nata ko yaya muka haɗa idanu sai yayi mun murmushi. Ni dai illahirin jikina a mace yake, zuchiyata sai harbawa take yi. Shagon gwala_gwalai muka shiga, abun mamaki saurayin Faty sai sawa yake yi ana cicciro sarƙoƙi manya_manya yana ta karawa a wuyan Faty. Da ƙyar suka ɗauki wata sarƙa da ɗankunne masu kyan gaske. Wannan aboki na saurayin Faty har za a mayar da sarƙoƙin a hallahesu, sai ya sa hannu ya ɗauki wata madaidaiciyar sarƙa mai mannen ɗan kunne, yace da me shagon. " Kam haza?" ( Nawa wannan) Ya tambayi me shagon, ya faɗa mishi kuɗin. Kuɗi ya zaro a aljihunshi ya biya kuɗin sarkar. Aka sa sarƙoƙi biyu a leda daban_daban muka fito. Daga nan sai muka wuce wani gidan cin abinci mai haɗe da ɗakunan kwana. Gurasa ce aka kawo mana da nono da ake dangwalar gurasar dashi, sai shinkafa kaza ( chicken biryani). Ni dai duk a takure nake ainun, ga kallo na masifa. Faty kuwa sai taɓe_taɓensu suke yi ita da saurayin nata, Sima kuwa a teburin wasu matasan larabawa yaje ya zauna abinshi, daga ƙarshe ma suka zame suka barmu daga ni sai Yariman kallo da murmushi ( sunan dana raɗa mishi kenan) "Ma sa'alti nis mi " ( Baki tambayeni sunana ba ƴan mata). Mafi arabiya ( ban iya larabci ba) Na faɗa mishi. "Halnastaɗi'ina antata kallami bil guggati ingiliziyya? ( Kin iya turanci to) Ya tambayeni yana ƙure ni da idanu. Ƙalil_ƙalil ( Kaɗan_kaɗan) "Halnastaɗi'u hannata kallam al'an ( Yanzu zamu iyayin magana)? Na'am ( E) Na faɗa a gajarce. "What bring's you to this country? ( Me ya kawoki wannan ƙasar)? Ya tambayeni tare da bani dukkan nutsuwarshi. I came to work ( Nazo aiki) Na sake amsashi cike da ƙosawar tambayarshi. " Wich tabe of work ( Wanne irin aiki?)" Na yi shiru domin bansan ma me zance mishi ba. Tambayoyin sun mun yawa, daga haɗuwa sai ya titsiyeni da tilin tambayoyi. Ina cikin zancan zuchi sai ga Faty ta ƙaraso tana gyara zaman rigarta. "Yi haƙuri na barki kina jira. Amman nasan Salim uban magana da bin diddigi bazai bar bakin ki ya huta ba. Dan ƙila har kakanki na huɗu ya tambayi sunanshi ko? Dariya ta bani sosai, haka dole na ɗan dara kaɗan. Saurayinta ne ya ƙaraso shima sai gyare_gyare yake yi. Bamu muka koma gida ba sai wajajen biyun dare. Har mun fito a motar Salem ya biyo mu. Ledar wannan sarƙar zinare ya muƙo mun. Tare da gyaɗa mun kai halamar in karɓa. Faty na kalla itama taimun nuni da in karɓa. Hannu nasa na amsa nace. Thank you very much ( Nagode sosai). Sai yai murmushi yace. Halnastaɗi'u annakuna sahibain? (Zamu iya zama abokai) Ya tambayeni. Cike da ƙosawa nace. Na'am" Sai naga yayi wani ɗan ihu tare da damƙe hannayenshi bibbiyu. Ni dai haka na ɗingisa na shige ciki. Faty kuma a wajen na barsu ko me suke taunawa ohon musu. Ɗaki na faɗa ina mayar da numfashi na. Ban wani jima da shigowa ba su Faty suka shigo tana dariya. "Kakarki ta yanke saƙa Iyabo. In dai neman kuɗi kika shigo ƙasarnan da zummar yi. Albishirinki ga mijin Aure sukutum kin samu. Salim yace dani in miƙa soyayyarshi gareki, kuma a yadda ya nuna wallahi sonki yake yi. Kinga kuɗi ya bani yace in baki kiyi siyayya" Kuɗin ta miƙo mun. Wanda a lokacin wannan kuɗi in aka canjasu izuwa kuɗi namu na gida najeriya zai iya kaiwa dubu ɗari. Dubu ɗari me darajar fin million ɗaya a wannan zamanin da kuɗi basu da albarka. To a lokacin kuɗi babbane dubu ɗari, baki na riƙe nace. Ke Faty bazan karɓi waɗannan kuɗin ba ko ba gaskiya ba? Domin bazai samu soyayyataba bazan iya aurenshi ba. Na baro masoyina a ƙasata, ina da yara, iyaye, ƴan uwa. Wannan sarƙar ma cike nake da taraddadin karɓarta. Da ƙyar Faty ta shawo kaina na yarda na amshi kuɗi da sarƙar, dan na miƙa mata nace ta mayar mishi ma ni bana so. "Sarƙar ki saka a wuyanki da'iman kar kiyi wasarere da'ita dan sai a sace. Kuɗi kuma ki adana abinki. Amman wallahi da nice Salim yace yana so da aure, da a mugun guje zan aureshi in watsar da rayuwarnan da nake ciki. Ke kuwa har wanne irin miji kika tanadarma kanki a gida najeriya da kika ƙi amincewa da Salim? Mazan mu sun banbanta da mazan Larabawa, ina miki kwaɗayin shiga cikin babbar daular da har muma zamu dangwali arziki. Akwai Alawiyya data zauna tare dani Balarabe take aure,itama daga Najeriya tazo aikatau, ya ganta tana aiki a gidansu kamar wasa ya aureta yaransu biyu du maza. Duk shekara iyayenta da ƙannenta suna zuwa aikin Hajji, iyayenta sun zama masu arziki. Iyabo ki zauna ki nutsu tsam babu fa wanda yaƙi daɗi" Ni dai nayi jigum inata faman jujjuya maganganun a kaina amman kaina yaƙi ɗauka. Soyayyar Yaya Hamma kawai nake ji tana dukan raina, ina kuma hasaso dimuwar da zai shiga in labarin soyayyata ko aurena da salim ya je kunnuwansu. Wata zuchiyar tace dani. "Ki tsaya kallon ruwa kwaɗo yai miki ƙafa. Kul ki yi nazari dan gudun yin ba wan ba ƙanin. Ki ƙi Salim, ki koma Najeriya batun soyayyarki da Hamma yasha ruwa, ko kiga Daso a gidanshi tunda dama ba furta miki kalmar so yayi ba. Ba wani alƙawari yardadde ku ka yi ba." Sai naji gabana yana dokawa da ƙarfi. Ni dai ji kawai nayi asuba tayi ina daga zaunannan ko kwanciya ban yi ba. Ina yin Sallah saina kwanta bacci. A cikin baccin naji ana ɗaɗamun duka, ina buɗe idanuna muka haɗa idanu da Hajiya. "Maza tashi ki haɗo kayanki, an turo mota zaki koma bakin aikinki." Bani da zaɓi haka na haɗa kayana na fito tsamo_tsamo. A fitowata sai gani ga Uwani kaciɓus. Tayi baƙi idanunta yayi zuru_zuru. Yanayin yadda na ganta a zahirin gaskiya hankali yayi matuƙar tashi. Hannun juna muka kama. Buɗar bakin Uwani maganarta ta farko tace. "Allah yayi zamu gana ne Iyabo. Amman kinga daga nan Najeriya zan koma, inaso in mutu a ƙasata cikin dangina da gatana." Kuka na fashe dashi nace. Uwani ki zauna a wajen Faty ki bani lokaci zan dawo bazaki koma ke kaɗai ba Uwani." "Dalla wuce ni ki bani waje, zaki tsayar dasu kina baiwa" Cewar Hajiya. Ina kuka ina waigen Uwani har gaban motar gidan aikina. Uwani ki mun alƙawarin ba zaki tafi ki barni ba" Ina faɗar haka na shiga mota. Ya ilahi. Azaba, damuwa, ciwon baya dana ƙirji babu irin wanda a ciki ban ɗanɗaneshi ba. Ga tunani Uwani daya addabi ruhina.✍🏻 MRS BUKHARI Su iyabo suna ganin jalala Aimun hakuri yanzu kam na dawo gadan_gadan har saina gama labarin da izinin Allah.🙏🏻 [06/08, 9:35 am] BADI'AT IBRAHIM: *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 ZEE MUSA COLLECTION 💃🏼💃🏼 Tana siyarda atamfofi da laces da shaddar da sauran kayan Yara da shoes and bags da material zee Musa collection ba, anan ta tsaya ba tana siyarda kayan kitchen da supplement da saurankayayakin masu inganci kaidai ka garzaya 🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️Kar ayi Babu Kai ko ka tuntibeta ta wannan number din kamar📞📞08029882667 nagodee 💃🏼💃🏼💃🏼 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 13 Sannan ga wani irin ƙunci daya aureni ko da yaushe saina zubar da hawaye. Zuchiyata ɗaci take yi mun ainun. Nayi iya yina dan ganin nabar wannan gidan aikin. Wallahi abun yaci tura, sunƙi saurarata fu, sai suturu da ɗan kuɗi suke bani. Dan a zahiri basu da matsala barsu dai da fi'ili irinna tsofaffi. Haka na share wata huɗu, a lokacin harna fidda ran barin gidan, na kuma san Uwani ta riga da ta tafi Najeriya ta huta abunta. Sai fa in keɓe kaina inta aikin kuka. Ana haka tsohuwar da nake ma aiki tazo ta sameni a kitchen tace in haɗa kayana zata kaini wani gidan in zauna zasu tafi yawon buɗe idanu ƙasashen turawa wata biyu zasu yi. Na dubeta na ɗan cakuɗa mata larabcin ina nunar mata ta mayar dani can inda ta ɗakkoni ni Najeriya zani. Ai nan ta shiga faɗa tana zagina. Shine take faɗamun Hajiya ce tace karta barni in sake komawa gidan, ta siyar dani sun biyata kuɗina dan haka na zama baiwarsu wacce suke da iko da'ita. Kunji wata ƴar duma_dumar fitina. Wasu zafafan hawayene suka gangaro a kumatuna take na soma ambaton Allah. Na kwashe kayana tsab na bi bayansu. Ina bayan mota a zaune ina ambaton Allah. Gabana yanata tsananta faɗuwa dai haka. To da safe ne lokacin, amman bamu muka isa ɗan ƙauyannan ba sai wajajen sha ɗayan dare. Wani ƙauyene me kyau muk iso, gasu da awaki masu ƙoshi da buzu buzun gashi. Wani gidan laka muka shiga, ta cikin gidan me kyau an ƙawatashi da abubbuwan gargajiya masu ƙawa. Babban falon gidan wata iriyar kujerar larabawace wacce babu katako, kamar fulo take irin manyannan da bango ake jinginata. Da wasu riɗa_riɗan Mata naci karo suna zazzaune. Sai naga wata baƙar yarinya a cinyar wata balarabiya. Yarinyar zata kai shekaru sha takwas haka, da na ɗauka ƴar Najeriya ce, ashe irin baƙaƙen kenya ne. Gata da buɗaɗɗen idanu. Abinda ya tsoratani yarinya babu kaya a jikinta daga ita sai ɗan diras da rigar nono, shigowarmu ne balarabiyar ta cire hannunta daga rigar maman yarinyar. Sai naji duk na ruɗe hankalina ya tashi ainun. Nan duk suka miƙe suna ma iyayen gidana sannu da zuwa. Ɗaya daga cikin matan ta nuna mun wajen zama, na ɗan dofana jikina. Madara aka kawo mana da romon nama babu magi sai warin tafarkuwa kawai. In da sabo na saba da wannan cima. Ni dai dan tsoro nace na ƙoshi. Iyayen gidana suka ɗan taɓa dai haka, kana suka fice abinsu.Ɗaya daga cikin larabawan sai ta mun maganar kurame tana mun nuni da in ɗakko kayana muje ta kaini ɗaki. Na bi bayanta zungui_zungui har zuwa wani ɗaki madaiaici da gado, harda durowar ajjiye kaya me kyau. Da larabci tace dani. "Wannan shine ɗakin ki da safe zan zaga dake kiga aiyukan da zaki dinga yi. Zamu biyaki sosai. Kuma zamu siyo miki kayan sawa bama son ƙazanta muna yawan yin baƙi sannan bama son hijabi, iyakarki dashi Sallah, irin wannan kayan zaki dinga sawa." Ta nuna mun zatinta. Gajeren wandone mai kwalliyar tsagu hagu da dama, sai ficiciyar rigarshi ko hannu babu duka mamanta a waje fa suke. A daren ranar na shiga damuwa mai tarin yawa. Bayan na rama sallolina ina zaune ina roƙon Allah sai ga wannan baiwar Allah ta shigo. "Ga kaya ki saka, saiki sameni a falo, zan Kai ki kitchen ki dafa ma baƙinmu Shayi" Kai na gyaɗa mata kaina kawai. A lokacin ɗaya na dare zata yi. Ban ɗaki na shiga nayi wanka na fito. Ina buɗe kayan sai naga wata yaloluwar riga gajera mai hannun shimi sai hular gashi. Na juya rigarnan yafi sau a ƙirga, da ƙyar na saka yadda ta fitomun da zatina sai naji kunya du ta kamani rigar ta matseni ainun iyakarta kuma guiwa. Ina tsaye wannan balarabiya ta shigo. Nayi sauri na kifa wannan hular gashi a kaina. Takowa tayi kusa dani tana ƙamshi cikin harshen larabci tace. "Kinyi kyau ƴar aiki. Dole a haka zaki dinga aiki a gidannan. Wuce muje in nuna miki kitchen" sim_ sim_ sim nabi bayanta har zuwa kitchen. Kayan shayin da kofuna duk dai ta nuna mun duk yadda zanyi. Na ɗaura shayin sai na soma wanke_wanke dan naga uban wanke_wanken dake kitchen ɗin sai naji gara in yishi in rage aikina na gobe. Shayi ya dahu na zuba a wata ƙatuwar buta mai kofuna guda sha biyu harda tiranta. Na ɗauka ina tafe ina harɗewa gabana sai faɗuwa yake yi. Tun kafin in ƙarasa falon nakejin waƙar larabawa na tashi, ga ihun mata inaji. Na jima a tsaye ina tunanin taya zan ratsa cikin mutane a haka. Ina hawaye na shiga. Kutsa kan da zanyi naga mata cike da falon. Wasu suna tsaye sunata rawa, kuma fa daga su sai rigar mama da ɗan diras masu wasu wawalniya sai rawar ƙugu suke yi. Wasu kuma suna zaune a kujeru suna ta shafar jikin junansu. Wani tashin hankali da na gani anayi, wallahi ba shiri na dire tiran shayin na zura a guje sai ɗakina. Na fige hular gashinnan na durƙusa ina kukan tashin hankali. A fusace naji an buɗe ƙofar ɗakin, wannan dai wacce ta bani kayane. Cikin zafin nama ta zabgamun mari ashe wai na fasa kofi ajjiye tirannan da nayi da ƙarfi. Ta dinga zagina tana mun barazana masu nauyiin faɗe. Haka ta figeni bata sakeni ba sai a tsaƙiyar falonnan. Jikina na rawa na dinga binsu da shayi, wasu su ɗauka, wasu su ɗaga mun hannu. Kunji wata ƙaddara kuma. Dana dinga aikin dafa shayi sai wajajen ukun dare suka barni naje na kwanta. Idona ƙyam kamar an soya gyaɗa. Abubbuwan da naga mata nayi a tsakankanin junansu ne ya tsaya mun daram a raina. Kenan nan gidan ƴan maɗigone, ko gidan karuwaine aka kawoni? Ni dai cikina ya ɗuri ruwa, akan sallaya na kwana ina roƙon Allah ya kareni. Da asuba inayin Sallah na tsiri aikin gidan ko ina kaca_kaca. Sai kwashe rigunan Mama da ɗan diras nake. Na samu leda na tattare na gyara ko'ina na tsabtace komai, wajajen sha ɗayan rana na dafa tea na haɗa da biredi na karya. Har wannan lokacin babu wanda ya fito ni kaɗai naketa ɓuruntuna, sai wata ƙatuwar mage da take ta guje gujemta ita kaɗai. Bayin Allah'annan basu suka fito ba sai wajajen ƙarfe biyu da rabi na rana. Mutum biyu suka zauna, sauran huɗun suna tsaye sunyi shigar banzar data wuce ƙa'ida sai suka ɗaura abaya a saman kayan. "Zamu fita, kafin mu dawo kiyi abinci, kuma ki gyara mana ɗaki, wanki ma duk yananan mun tara" Cewar ɗaya daga cikin matan da naji ana kiranta Basma. Da harshen larabci take maganar. Tana dasa aya suka fice. Biyun dake zaune a kujera suna kallon wani shiri na batsa suka ce in haɗo musu Karin kumallo. Da sauri na fita, matane a cikin akwatin talabijin ɗin sirara suna rawa. Ni dai ina hawaye na dafo musu shayi na turara musu gurasa na kai musu. Ɗakunan kwanansu na wuce, nan na shiga aiki ka'in da na'in dan Komai a zaune yake daram, ni na kintsa komai. Na buɗe sib duk na hallage musu dogayen rugunansu. Ina wannan aikin fa na kunna injin wanki ina wankewa ina busarwa. Sai la'asar na kammala. Ba zama na soma guga, ga girki ina tashi ina dubawa, kafin magriba dai na gama komai, da nayi Sallah sai na ɗan kwanta. Gabɓaina babu inda baya nishin ciwo. Ƙofar ɗakin aka turo da ƙarfi. Idanuna na sauke ganin irin kallon maitar da take yi mun tamkar mage taga ɗanyen kifi. A hankali take takowa duk takunta sai inji gabana ya sake tsananta bugawa. " Anti jamilatun wallah, A ti hibbina ni? ( Kina da kyau wallahi kina sona?) Kalmar sai naji tayi mun wani gingingin a kaina, tunda nake ban taɓa tunanin mace zata iya irin wannan muryar mai kashe jiki ga ƴar uwarta mace ba. Ɗan manuniyarta ta ɗora a wuyana tana mun tafiyar tsutsa izuwa wushiryar data raba mamana. "Ma qulti shai'an Jamilatun? ( Baki ce komai ba) "A ti hibbina ni? ( Kina sona) Ta sake maimaitamun. Ni dai na kasa furta dai_dai da kalma, jikina ya mutu tuɓis rokon Allah da nadamar baro ƙasata ta gado ya sake ɗarsuwa a zuchiyata, tsanar wannan mata sai ninka kanshi da kanshi yake yi. " Khus mala bi si ki ( Karɓi kayanki) Ta miƙo mun babbar ledar dake hannunta. Nasa hannu cikin ƙosawa na amsa. Shukran jazilan ( Nagode sosai) Iyakar abinda na faɗa kenan, harta kai bakin ƙofa tace. "Ismi Kariya" ( Sunana Kariya) Sai ta fice, na saki wawuyar ajjiyar zuchiya. Na kasa tsaye na kasa zaune, da dai naga babu sarki sai Allah saina fita falo da zummar zuwa kitchen ɗakko abincina. Da wannan riga fa iya guiwa da aka bani fa kar ku mance duk nake wannan zurunkaɗanar. Ina shiga falon naga Kariya da Aliya suna aikata ɓarna. Gyaran Murya nayi musu, ko a jikinsu ina waige harna isa kitchen. Tsabaragen takaici a kitchen ɗin nayi zamana naci abincin wallahi nayi kwanciyata a kan tayil a wajen na kwana bani na farka ba sai asuba. Nan ciwon bayana fa ya tashi kunsan sanyi yanda yake tada ciwukan ƙashi ( khadija maidoki wai sanyi na tada ciwukan ƙashi?) A taƙaice sai Aliya ce ta taimaka mun na iya miƙewa, Sallah sai a zaune nayi ta. Ranar dai banyi aiki ba sai washe gari da na ɗanji dama_dama. Haka rayuwata taci gaba da gudana cikin wannan kazanta da tashin hankali. Babu irin abinda ni Iyabo idanuna basu gane mun ba. Suturar banza ni kaina dole haka nake sanyawa inta hidimar aikina a hakan. Allah ya ga zuchiyata ba"a son raina bane. Tsorona Allah tsorona kar in gudu in faɗa mummunan hali, amman wallahi da zan gudu, kuma ina tunanin Uwani ko tana can tana jirana kota koma najeriya ne, duk ban sani ba. Babu rana mafi muni da tashin hankali data wuce ranar da Kariya ta zo ɗakina cikin dare da burin kasancewa tare dani. Dama ta jima tana tattaɓani haka tana bani kuɗi. Tayi tayi in saki jiikina da'ita amman Allah yana kuɓutar dani daga sharrinta. Sakamakon adda'a dana tsananta yi babu dare babu rana, cikin Sallah ko cikin aikin bautar da nake yi babu lokacin da adda'a take barin bakina. Ina kwance akan sallaya bayan na gama ƙiyamul laili, sai naji kamar a mafarki ana rabani da suturuna dai haka. Kasancewar jikina ko da yaushe a tsamane yake da kafirar gajiya, dole baccina zai kasance mai nauyi, kuma dama bana yi ma da wuri shi baccin. Wallah duk abubuwa da sukaita wakana cikin mafarkina nake jinsu a nawa wautar. Ashe a zahirance suke faruwa dani ni Iyabo. Dare mafi baƙi a gareni, jin hannu da bakin Kariya a inda bai dace ba shi ya dawo dani na kasance a farke. Kaina yaso tarwatsewa baki ɗaya ma. Wuƙa ta zaro a rigar Mamanta ƴar ƙarama, sai kawai ta tsaga mun gefen fuskata. Ko zafi banji ba, dan tafasar da zuchiyata take yi kan abinda take aikatawa dani yafi mun zafi, fiye da yankan wuƙar. "Bana so kice komai. In kika yi yinƙurin yi mun gaddama kasheki zanyi in tona rami in burneki a gona. Kibi umarnina in ƴantaki" To a gaskiya na tsorata da kalamin Kariya, kuma ba barazanace take yi mun ba da gaske take nufin zata kasheni. Maganganun Faty ne suka dawo kaina da labarin yanda wasu daga zuwa gidan aiki ba a sake jin ɗuriyarsu har abada, sai dai iyayensu dake gida najeriya suji shiru. Idanuna a runtse harta gama komai. Kuma abu mafi wahala da ɗaga hankali shine umartata da tayi kan in yi mata sak abubuwan da tayi mun. Naso in turje, sai tayi sauri ta zaro wuƙarnan ta sake kawo mun yanka. Cikin zafin nama na kauce. Babu shiri na soma yi mata abinda take so. Allah ya ga zuchiyata ina mai ƙyamatar dukkan abinda nayi ma Kariya, da dukkan wanda tayi mun. Tun daga wannan rana saina samu rangwame, yawan aiki sai ya ragu mun. Ni dai a kullum ina roƙon Allah akan ya kawo mun mafita, ya kuɓutar dani daga wannan rayuwa baƙa. Nan fa gaga _gaga al"amura suka ci gaba da tafiya a baibai, har wata biyu ta cika. Sai na ke tambayar Kariya yaushe iyayen gidana zasu zo su ɗaukeni ne?. A lokacin muna banɗaki inai mata wanka. Buɗar bakinta sai cewa tayi. "Na siye ki a hannunsu kamar yadda suka faɗa mini suma siyanki suka yi. Abinda nake so dake shine ki cire tunani da mafarkin Najeriya a ranki, ke da Najeriya har abada" Ai sai kuka, sai zazzaɓi, daga zazzaɓi sai babbar jinyar da hatta abinci sai Kariya ta bani a baki. Kuma ta kira likitansu yazo ya dubani. Sati na biyu cur idanuna kullum cikin danshi suke. Wata rana ina aiki a kitchen Kariya ta shigo take sanar dani zasu je Umara in zauna in kula da gidan. Harta juya cikin tsoro nace. Uridu an azhabu ma'akum ila Umara billah. ( Inaso in biku umara dan Allah) Ƙur ta yi mun da idanunta, da Allah ya ɗaurani a kanta sai ta amince mun. Cikin murna na sako kayan jikina na bisu. Muna tafe a mota ina kallon gari, ina lure da komai ina sassaka amala a ko wanne kallon kan titi. Tafiyar bata wasa bace, cikin amincewar ubangijina sai gani a Ka'aba har a jikinta. Kuka na fashe dashi inata roƙon Allah yafiya dan gani nake yi Allah bazai yafe mun kan ƙazantar da ake sani yi dan dole ba. Adda'a nayi na maimaita babu iyaka. Zuchiyata saita samu salama da nutsuwa yau na yi umara gani a ɗakin Allah. A hotel ɗin wajen Harami muka kwana kafin kuma muka koma gida. Naga ƴan ƙasata najeriya, nayi magana dasu na samu farin ciki. Na barbaza idanu ko Allah zaisa in ga wanda na sani a kamfaninmu amman Allah bai haɗamu ba. Amman na samu nutsuwa a zuchiyata in sha Allah na kawo kukana gindin maganin. Allah cikin ikonshi kwana biyu da dawowarmu Umara, da daddare na zage na yima Kariya abinda tafi so, sai murna da daɗi take ji, Allah sai ya matsi bakinta tace. "Zan miki duk abinda zai faranta miki. Zan iya miki komai. Da hikima nace da'ita. Inason ki kaini kamfani zan tura da kaya Najeriya akwai masu tafiya, kuma zan tura ma ƴan uwana da kuɗi" Allah mai yin yadda ya so, sai ta amince ba tare da tayi tunanin komai ba. Ni kuwa a cikin daren na haɗe kayana tsab a wani ƙaton akwati ko tsinke ban bari ba. Kuɗaɗena dama suna ɗamare a marata. Na mance ban faɗa muku ba har setin ɗan kunne da sarƙa, awarwaro, zobe, chain ɗin ƙafa Kariya ta sai mun masu darajar gaske. Washe gari sassafe ta kira uwar ɗakina wannan tsohuwa data kawoni, ita tai mata kwatancen kamfani. Ta kira wani saurayinta ya zo da mota ya kwashemu, da tarin kayana dan na samu alkhairi sosai a gidan. Tafiya muke, ni dai adda'ace kawai a bakina, gabana sai yankewa yake yana ta fa faɗuwa gani nake kamar za'a samu matsala. Tafiyace ashe bana wasa ba a gabanmu, a hanya mu ka yi azahar muka yi la'asar. Muna zaune a wani ƙauye gidan cin abinci sai ga kiran wayar Aliya. Ina jiyo duk abinda take faɗa dan a lokacin harshena na larabci yayi ƙarfi sosai. Sai hantar cikina ta soma tsittsinkewa dan tsoro, gudawa ta taru a cikina. Wani irin mugun kallo Kariya ta watsa mun bayan ta ajjiye wayar. Babu abinda nake ambato sai Allah, nasan shi ne kaɗai zai taimakeni a kan duk tsananin da zan shiga. "Me yasa kike tunanin ni zaki yaudara ki gudu?" Ta furta da harshen larabci. Sai da na ambaci Allah kafin na ɗaure fuskata nace. Na sanar dake komai tun kafin mu fito. Kaya zan tura Najeriya a ajjiyemun. Kuma a hakanma zanje in yi siyayyar kaya in haɗama wacce zata tafi duk a tafi mun dasu. Ba guduwa zanyi ba" Na ƙarashe maganar tawa da sarƙewar harshe. Ta dai nuna kamar ta gamsu da bayanina tunda har muka kama hanya. Bamu muka iso ƙofar gidan da muke ba sai wajajen 1 na dare. Muna isowa wata mota itama tana parker wa kamar tare muke. Faty ce naga ta fito a motar tana tangaɗi kamar mai jin bacci. Da sauri na ɓalle murfin motar na fito. Na sakko da bataliyar kayayyakina. Faty tana hangoni sai ta zo tana fara'a. Bansan sanda na rungumeta muka saka kuka dukanmmu ba. Ashe Saleem da saurayin Faty sun iso daf damu bamu sani ba ma. "Iyabo kice kika ƙare haka, ashe kina raye Hajiya tace kin mutu?" Murmushi nayi nace da'ita. Ban mutu ba ina raye, mummunan hannu na faɗa amman Allah ya kuɓutar dani." Ba sai na jiyo na dubi Kariya nace da'ita. Ni na dawo gida kenan babu ni ba ƙasar Saudiyya ma baki ɗaya Najeriya zan koma" Ranar naga tashin hankali dan Kariya sai ta soma daddannamun ashariya tana fincikata kan lallai sai mun koma. In ba haka ba zata kira askarawa su zo su kamani. Da rikici yaƙi ya ƙare sai Salim ya mun nuni da in koma gefe. To a lokacin har matan gidan namu sun soma fitowa. Cikin hukuncin Allah sai ga Uwani itama ta fito sai raba idanu take. Karab muka haɗa idanu mu kai ma juna murmushin farin ciki. Tana ɗingishi ta ƙaraso kusa dani muka riƙe hannun juna gam tamkar ance za a farraƙamu. Rikici fa ya kai har Hajiya ta fito. Tana ganina itama fa tace. "Baki isa ki koma mun cikin gida ba. Sai dai ki nemi inda dare yayi miki. Har ke Uwani kar wacce ta koma mun cikin gida" Tana faɗar haka sai tace da Kariya karta yarda ta tusani gaba sai mun koma" "Ku shiga mota dake da ƴar uwar taki zan kai ku gidana" Cewar Salim wanda ranshi ya gama ɓaci. Faty ce ta ja hannuna muka wuce ni kuma ina riƙe da hannun uwani dama. "Uwani bari in ɗebo miki kayanki, tunda muguwar matarnan ba barinki zata yi ki shiga ba" Faty amman dake zamu tafi ko? Ni fa tsoro nake ji, kuma wallahi Najeriya zan koma" Ƙur ta dubemu can kuma tace. "Shikenan zan biku har saina tabbatar kun tafi Najeriya sai in dawo, yanzu dai ina zuwa" Nan ta tafi ta barmu, ni ai saina haɗe kaina da guiwata na dinga dirzar kuka kamar raina zai fita, Uwani ma sai shessheƙa take yi. Kayanmu su Salim suka lode a bayan Bot, Faty ta shigo mota muka ɗauki hanya. Salim sai roƙona yake yi akan in daure in yi shiru ya'isa haka. Amman ina wani baƙin ciki da nadamar zuwa ƙasar ke turniƙeni. Duk mun lalace mun faɗa balaoi iri da kala. Tafiyar da mu ka yi bata wuce tafiyar awa ɗaya ba sai gamu a wani katafaren rusheshen gida, mai yalwar filin tsakar gida. Salim na gaba muna biye dashi a baya har zuwa cikin babban falon gidan, inda ya kasance matattarar ɗakunan gidan, da ƙafar bene da zata sada me hawa izuwa sama. Babu kowa a falon a lokacin da muka shiga. Har ya kama ƙafar benen sai ya soma kiran sunan Atika, Atika. Allahu Akbar sai ga wata ƴar burkina fasu ta tawo a guje har tana tuntuɓe jikinta da uniform na masu aiki. Yace ta haɗo shayi da abinci ta kawo mana ɗakinshi. Nan muka haura tiryan_tiryan har izuwa ɗakinshi daya kasance madaidaicin ciki da falo mai shaƙe da kayan alatu. A irin kujerarsu mai daɗin zama muka zauna duk a takure ni da Uwani Faty kuwa a cinyar saurayinta ma tayi zamanta tana yi mishi raɗa a kunne. "Ku saki jikin ku nan gidanki ne ƙawata. Ummi da Abi sun fita, gobe zan haɗaku dasu ku gaisa." Mun gode sosai Allah ya saka da Alkhairi. Faty kema babu abinda zamu ce dake sai godiya" Na faɗa jikina a sanyaye sosai. Waje saurayin Faty da Salim suka bamu, mu kai wanka muka kintsa, na rama sallolin da suke kaina. Sai ga shayi da shinkafa da romon nama Atika ta kawo mana. Bayan munci ne Faty tace. "Yaya akayi Hajiya tace damu kin mutu Iyabo?" Ɗan dariyar takaici nayi musu nacce. Sabida ta siyar dani ba. Kuma ta basu uwarnin karsu sake su barni in fita ko ƙofar gidane. Duk da inna fitan bansan inda zan dosa ba, ina tsoro da gudun faɗawa matsala" Nan na soma labarta musu baƙar wuya da azabar da na sha, da ƙazantar dana tsinci kaina a ciki na ƙarfi da yaji. Uwani ta fashe da kuka tace. "Nima haka na samu wata uwar aiki ta dinga tursasani irin ƙazantar da aka saki a ciki. Iyabo naci baƙar wuya. Kinga dama ni tunda labarin mutuwarki yazo garemu na yanke yin waya da su Hajiya, da Hafizu da yaran duka. Dan na yanke har abada bazan koma Najeriya ba. Dan bansan me zance ma danginki ba" Ina hawaye nace Sake komawa gidan aiki kika yi bayan rabuwarmu dake da nace ki bani wata ɗaya zan dawo?" "Gidajen aiki har uku ma masu mugun hatsarin gaske. Amman babu abinda zamu ce da Allah sai godiya. In sha Allah daga nan sai gida Najeriya. Kuma na gode Allah nayi Umara har sau biyu. Kefa kin samu wannan damar?" Ta tambayeni da karshashiin son jin amsa. Idanu na lumshe na buɗe. Na samu damar yi sau ɗaya. Alhamdulillah. Bani da burin daya wuce in sa iyayena da yarana a idanuna. Nifa tunda nazo ƙasarnan sau ɗaya tak nayi wayaa da Burodami Debisi " Faty tace. "Ai kuwa wani mai suna hakan ya kikkira wayata. Sai wani mayen Hamma da duk bayan kwana biyu sai ya kira wayata yanaso yayi magana dake" Idanuna na lumshe soyayya da kewar Yaya Hamma suka dirarmun a zuchiyata farin ciki ya kamani. To ku aramun waya in kirasu. Allah sarki Yaya Hamma ɗan amana ashe ina ranshi kamar yadda shima yake raina" Faty ta miƙo mun wayarta tana daga kwance. "Banyi serving number shi debisin ba. Amman na seving ɗin ta Hamma guda ɗaya. Dan lambobi daban_ daban yake kira dasu. Daga baya ne yace in save ɗin wannan, in kin zo in baki shine layinshi. To shine dawowar da baki yi ba sai yau" MRS BUKHARI 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 14 MARAƊI Gwadabe: "Amarya ba kya laifi ko kin kashe ɗan masu gida. Ina fatan kin wayi gari cikin aminci?" Ya faɗa mata cikin raɗa_raɗa. Kanta ta sauke zuwa ƙasa kana tace. "Alhamdulillah mijina, da fatan kaima kana cikin ƙoshin lafiyar kamar yadda nake? Murmusawa yayi kaɗan ya jawo hannunta zuwa bakin gado. Daya zauna saiya ɗorata bisa cinyarshi yana wasa da yatsunta. "Hadiza babu abinda zance dake sai dai ince Allah yai miki albarka. Kin kaini wata sabuwar duniya da ban, na gaisheki kuma na yaba da ƙoƙarinki, ya farantamun. Wani daɗine ya lulluɓe Hadiza irin daɗin da ya kasa tsayawa iyakar zuchiyarta. Kallonta yake yi hankali a kwance. A zahirin gaskiya Iyabo ce ke mishi gizo a idanunshi, tare da tunano daren farkonsu, da irin romon soyayyar daya kwasa a jikin Iyabo. Gata mai ƙiba jiki duk laushi da ƙiba. Idanu ya lumshe kawai, haƙiƙa bai taɓa tunanin akwai abinda ka iya rabashi da Iyabo ba face mutuwa. Ashe ƙaddara tuni ta rubuta ƴaƴa ukune kacal a tsakaninsu. Domin kuwa yasan har abada aurenshi da Iyabo ya mutu bazai dawo ba. Tamkar yadda ba'a taɓa mutuwa an dawo ba. "Nace ba. Tunda matar abokinka sun tawo da yara. Me zai hana kawai su zauna ba sai ka sha wahalar zuwa ɗakkosu daga baya ba?" Ajjiyar zuchiya ya sauke kana yace. "Zamu tattauna dasu zuwa anjima inna samu kaina. Yanzu wanka nake so in yi, in fice dan yanzu zaki ga gidan ya kuma ɗinkewa da mata." Miƙewa yayi ya soma shirin wanka. Hadiza ce ta zuba mishi ruwan wankan a bokitin ƙarfe. Kafin ya fito ta ƙarashe gyare_gyarenta. Yana fitowa yace. "Zan shiga cikin gida. Sai zuwa dare zan shigo. Ki shirya zan haɗaki da amaryarki." Fuskarta ya shafa yana murmushi, dan ya hango kishi kwance a idanun. Har ƙofar ɗaki ta rakashi, a madadin ya fita, kamar yadda yace da'ita. Sai ya faɗa ɗakin Amarya. Hadiza tayi murmushi kawai ta komawarta ciki. Tana shirin shiga banɗaki dan ta wanke. Sai ga Balaraba ɗauke da tiren abincin kari. "Amarya uwar gida kuma irin wannan ɗaukar wanka haka" Murmushi Hadiza ta sake. "Ke dai bari Balaraba. Tun ɗazu nake jiran yara ma su shigo su samo mun gaushi a cikin gida, inason yin turaren wuta." Balaraba ta ajjiye tiran hannunta a gefe tace. "Tunda zan sake dawowa kawo ma amaren gidan abinci. Bani kaskon ki yarinya in ciko miki da gaushi" Dariya Hadiza tayi, ta ɗakko kaskonta mai murfi taba Balaraba ta fita. Ita kuma ta faɗa banɗaki ta wanke tas. Kamar an tsikareta ta faɗa kitchen ta soma canja mishi fasali. A kitchen ɗin Balaraba ta sameta ta miƙa mata kaskon cike da gaushi. Kafin kace me Hadiza ta bunke ɗakinta da turaren wutan daya tashi kan amaren gidan, harma da maƙota, wanda su kiya daga Najeriya a hannun Mrs Bukhari gidan ƙamshi. ( Turarene mai tsada na isassun mata. Sau ɗaya zaki turara ɗakin ki dashi amman zai kai sati yana ƙamshi. In kika siya gidanki bai kai sati yana ƙamshi ba. Ni Mrs Bukhari gidan ƙamshi zan dawo miki da kuɗinki) Shafa data jiyo wannan ƙamshi na turaren wuta sai taji ta raina ƙamshin turarukan wutanta da take tunanin zata yaƙi matan Nijar dashi. Damma bata san daga asalin ɗakin da yake fitowarba. Ji kake kawai ana wannan turare ba dai ƙamshi ba. Hadiza tana zaune tana shan farfesun rago sai ga Aminiyarta Luba ta shigo riƙe da hannun ƙaramin yaronta, ɗayan hannu riƙe da ƙatuwar leda shaƙe da kayayyakin ɗa'a inji katsinawa, kayan mata inji Kanawa, maganin mata inji jasawa. "Ashe wannan ƙamshin daga ɗakinnan yake fitowa Hadiza? A gaskiya ban taɓa jin ƙamshin turaren wuta irin wannan ba. Banga laifinki ba yanzu da kika nace ke sai kayan ƙamshin MRS BUKHARI ba. Matar tasan aikinta. Amman dai ƴar maidugurice ko, wannan ƙamshi ya gigitani" Dariya Hadiza tayi ta kamo hannun Luba. "Zauna ƙawata. In dai kayan Mrs Bukhari ne baki ji komai ba, tunda baki shaƙi humrar matan aurenta ba" Zama tayi tana kallon Hadiza. Hannunta da Hadiza ta kama ta shinshina babu shiri ta lumshe idanunta, ƙamshi mai ni'ima ta daki hancinta. "Wannan humra kwai ƙamshi Hadiza" Dariya Hadiza ta kuma sakawa tace. "Kajita, ai humrorinta sunfi da nan. Wannan ƙamshin turaren turara jikine mai riƙe fata kita ƙamshin ƴan kanuri. Luba Mrs Bukhari Kanuri ce, kuma a kayanta babu ha'inci, shi yasa zaki ji kuɗin kayanta ya bambanta gaskiya. Amman muddin kika siya zaki san yaci kuɗinshi. Taso muje ciki in nuna miki humrorinta na jiki, dana gashi ki gani" Ba shiri Luba ta biyo bayan Hadiza, harda sunkuto tiran kayan karin da Hadizan take yi. Gaban mudibi ta kaita. "Kinga wannan humrar matan aurece, ko kishiyarki ba'aso ta shaƙa domin humrace mai sirri" Zaro idanu Luba tayi. "Kaddai kice mun ta asirice, yaushe kika zama haka Hadiza?" Hadiza ta dafa Luba. "Bata asiri bace, ba,a yita da rubutu ba, ba'a yita da wasu surorin Qur'aniba, babu wani surkulle tattare da duk kayanta wallahi sai aiki. Domin ba da ka take haɗa kayayyakinta ba. Sirrin itatuwan mallakar miji sai Kanuri tarihi yasan da hakan. Tasan me zata haɗa da me ya bada kwanciyar hankali. Ƙamshi shi kaɗai rahamane, kuma shi kaɗai zai sa mai gidanki ya yarda dake. Kinga wannan kulaccam ce, wato man ƙamshi me gyara fata tayi laushi tayi ƙamshi. Ko zufa kika yi ƙamshine zai dinga fita. Wannan humrorine masu sirrin ƙamshi kin gansu. Wannan turaren turara ɗakin kwanan Oga ne domin saukar masa da duk gajiyar daya ɗebo a waje, in ya fita kuma yaji bashi da wata nutsuwa data wuce ya ganshi a gidanshi. Waɗannan turarukan wutane iri daban daban, kuma suna da lokutan kunnasu. Ga turaren gashi, ga kulaccam ta gashi, mai sa tsayin gashi, taushi, da ƙamshin gaske. Ga turaren turara gashi, gana turara jiki. Wannan sunanshi gam. Turaren tsugunnone mai maida tsohuwa yarinya. Ga_ga_ga. Hadiza ta dinga jero mata bayani. "Ya isa Hadiza yaushe zaki saka odar wasu kayan ni dai inaso da gaggawa, kuma zaki ɗan samun dan Allah?" "Kwantar da hankalinki zan sammiki. Oda kuma dama akwai kuɗaɗe a hannuna, ki kawo naki saimu tura mata kuɗi ta nita, kayanmu zasu iso cikin aminci. Tana da kostomomi sosai a kasar Nijar sosai, kinsan ƴan Nijar suna son kaya masu kyau da inganci. Tsadar abu in dai mai kyaune baya damun mu" Nan suka zauna zaman cin abinci kuma. "Ga magungunan ki nan, tukuɗinma an daka miki garinshi da dama, saiki dinga samun lafiyayyen Nono kina damawa ki sha. Gasu tsumi kala_kala harda maɗi, akwai na matsi ma. Kinsan lamarin maza sai ka dage barinma ace kana da kishiya kuma budurwa. Sai fa ka dage sosai. A kwana bakwai da zaiyi a ɓarayin Amarya kiyi ƙoƙarin tsuma kanki sosai. Kinga acan ya shiga sabuwar duniyane daban. Kema saiki sabunta baiwar da Allah yai miki. Ita mace tana son sabis lokaci zuwa lokaci inba haka ba, sai kiga injin ɗinta yayi tsatsa, shi kuma tsatsa kashe ƙarfe yake yi duk kyansa, sai ana sabis ana zuba injin oyal." Dariya suka saka dukkansu. A haka dai gidan ya ɗinke da jama'a. Ƙawayen Hadiza na makarantar da take koyarwa suma sai yau suka haɗo kansu suka zo. Kuma suka tawo mata da goma sha taran arziki. "Hadiza ya kamata ki shige gaba muje ki kaimu wajen amaryarki a matsayinki na Babba. Dan na sanki da ɗan banzan kishi. Ya kamata ki watsar da zafin kishi ki bi hanyoyin dabaru na zamani, wanda babu cutarwa, baki da laifi har a wajen Allah " Cewar Madam Chima ƙawa ga Hadiza kuma itace uwar gida a gidanta tana da kishiyoyi har uku. Amman kab cikinsu babu wacce bata sha gabanta ba a wajen miji. Kullum madam Chima mijinta ke goyota a moto ( mashin kenan suke nufi) ya kawota makaranta. Kuma duk abinda yake yi da zaran lokacin tashi yayi zai tawo ya mayar da'ita gida. Hadiza tace. "Ni ai har wayewar garin yau bansan wacce kalace Amaryar ba. Ni ai tunanina ita ya dace tazo ta gaisheni tunda itace ƙarama" Chima tayi shewa tace. "Baki san takan duniya ba. Ai zuwan da zaki yi kankaro mutuncinki zaki yi a wajen mijinku. Ke dai sheƙa kwalliya kisa kaya tsadaddu muje kinji?" Akace mutum baya ƙin ta mutum wai ance da ɓarawo ya ruga. Duk wayonka da dabararka in kaga wani sai kace wannan malaminka ne a komai. Hadiza ta shirya tsab cikin baƙar shadda wacce tasha surfani irinna al'adar ƙasarsu, ta sanya ɗan kunne da sarƙar zinaren da Malam ya basu, ta ɗauko farin takalmi dake cikin akwatin da taima kanta ta saka. Tabi jikinta da humrar Mrs Bukhari, kana tabi kayan jikinta da turaren fesawa na tufafi mai sanyin ƙamshi shima daga Mrs Bukhari ( kina so ƙamshinki ya zam na daban a rasa da kalar turaren fesawan da kike amfani? Ko kuma kyauta kike so na musamman ki baiwa maigida na turare mai sanyaya ruhi kuma kin rasa wanne kikeso? To ina da turaruka na fesawa da nake haɗawa masu sanyi da taushin ƙamshi na mamaki. Hajiya daga yanzu babu ke babu siyan turare Designer babu ke babu zuwa kanti siyan turare. Zan haɗa miki turare naki na karan kanki wanda in kasuwa za'a karaɗe ba za a samu me irin ƙamshin naki ba. Gashi da riƙe tufafi har ki wanke tufafinki bazai bar ƙamshi ba.) Gaba ta wuce ƙawayenta suna biye da'ita a baya har zuwa ɗakin Amarya. Da sallama suka shiga, kafin su ƙarasa shiga falon har ƙamshin Hadiza ya cika falon ya doke turaren wutan da aka turara ɗakin Shafa, dama turaren cikin akwati da ita Shafar ta fesa. Hadiza da Shafa idanuwansu ya sarƙe dana juna. Dukkansu sai suka tsinci kansu cikin damuwa da rashin ƙarfin guiwa cikakke. A fakaice Hadiza cikin sakanni ta karance irin kayan alatun da aka danƙara a ɗakin Shafa. Muryar Ayashe ce ta dawo da Hadiza cikin doka da oda. "Uwargidanmu ga waje ku zauna. Yanzu muke shirin mu kai Amaryar ma ɗakinki sai gashi kin rigamu ma zuwa" Yaƙe Hadiza tayi wanda ya gyara mata fuskarta cikin sakewar murya tace. "Ai babu komai nasan sha'anin biki anata fama da jama'a. Ni ɗinma tun ɗazu naso shigowar." Nan ɗakin ya kacame da gaishe_gaishe a tsakanin dangin Shafa, da ƙawayen Hadiza. A sanyaye Shafa tace. "Yaya ina kwana, ya akaji da jama'a?" Hadiza taji wani abu ya daketa a zuchiyarta yadda taji Shafa na karya harshe wajen lafazi. Bama Gwadabe ba hatta ita salon muryar ta burgeta. "Lafiya lau Amarya ya baƙunta" Wata tsohuwace ta katse maganar ta hanyar cewa da Hadiza. "Dama yanzu zamu kawota wajenki, mu shiga da,ita cikin gidan surukan nata, da manyan gidan. Dan gobe asubar fari zamu kama hanya, anjima kuma zamu leƙa kasuwa muga gari. ( Kunsan ƴan ƙauye akwai son shiga kasuwa ko ba zasu sayi komai ba zasu je suita zare ido) Miƙewa Hadiza tayi tare da yi musu sallama. Shafa tabi Hadiza da idanu ta baya. Dirarriyar mace doguwa son kowa. Kanta ta sauke ƙasa yayin da zuchiyarta taci gaba da harbawa. Ta bangaren Hadiza wannan yanayin ma yafi ƙarfi dam ita sai da ƙwalla ta taru a idanunta. Basu jima da komawa ɗaki ba sai ga sallamar dangin Shafa sun tusota gaba. Tana saye da riga da siket na atampa ɗinkin yan Abuja da wata sarƙa da ɗan kunne fashion me kalar atampar. Mayafinta da takalminta su kuma iri ɗaya amman ko kusa babu kalar a jikin atampar. "To Hadiza ga Amanar Shafa mun danƙa a hannunku ke da Gwadabe. Dan Allah ku zauna lafiya ku rungumi mijinku banda tayar mishi da hankali. In kika ga Shafa tayi wani abun ba daidai ba a matsayinki ta babba wacce ta fita shekaru da hangen nesa sai ki nushetta. Ke kuma Shafa duk abinda zamu faɗa mun riga da mun faɗa miki. Kiyi musu biyayya, kinga a ƙasarnan baki da kowa sai su, duk abinda abokiyar zamanki ta gyara miki ki gyara. Ni da Mahaifiyarki tsawon zaman kishi na shekara hamsin da mu ka yi a tsakanina da'ita girmamawane. Yaya sama, Yaya ƙasa, kuma duk abinda Yaya ta sani shi nake yi. Mu kai zamanmu salamun_salamun dan Allah Shafa kiyi koyi da irin tarbiyyar gidanku" In wannan yayi sai ya cika, wannan sai ya kama. Haka dai sukaita yi. Hadiza tace. "To Allah ya bamu ikon riƙe wannan amana. Allah ya bamu zaman lafiya da fahimta a zaman?" Nan su kai mata sallama kuma. Daga nan su ka kaita ɗakin Yaya Tasi'u shima suka danƙama Anty Badi'a amanar ta musu ido akan zamantakewar. Ita ta rakasu ɗakin matar Jamilu. Sai gatsina take tana magana ciki ciki dai. Daga nan Anty Badi'a ta jagorancesu zuwa dukka ɗakunan amaren gidan, daga nan suka shiga cikin gida shima suka zagaya du ɗakuna huɗun tas. Cikin gidan Malam Anata hada_hadar ɗaura girkin rana. Yayin da baƙin da suka taso daga nesa suketa haramar komawa garuruwansu tunda dai biki ya ƙare. Baba Suwaiba da Amaryar Malam suna dai cikin danginsu anata hada hadane. Amman zuchiyarsu a cike take tab da tsoro da fargabar Malam. Malam ya ɗauki zafi sosai, hatta gaisuwarsu yau Malam yaƙi amsawa abinda bai taɓa yi ba kenan. Kuma ya sake jaddada musu lallai su zauna da zaman shirin dole zasu tafi gidajensu. Kafin ace abinci ya nuna tuni rabi da kwatan baƙin biki ko wacce ta kama gabanta, sai tsirarin ƴan uwa da su kai ragowa su kuma sai zuwa gobe zasu watsr. A ɗakin Baba Suwaiba duk ƴan uwanta sun watse. Amaryar Malam kuma dama mutum ukune suka zo daga ɓangarenta, sai ƙawayenta na maƙota, kasancewar ba ita ke aurarwa ba. Ɗakin Baba Fhatsima ma Altine da Balarabane kaɗai su kai saura, sauran dangi su ana gama karin kumallo ma suka tattare yanasu yanasu suka kama gabansu. Ɗakin Baba Asshine yake cike da jama'a sosai dan su ko soma raguwa ma basuiba. Ƴan takai ma su Laila suna nan, sai su Ayashe, da dangin Amaryar gwadabe, da su Bara'u wanda su kuma gobe zasu kama hanyar suma. DAKIN BABA FHATSIMA:. Balaraba sai faman gyarama Baba Fhatsima ɗaki take yi, ko ina kaca_kaca shine take son ta gyara komai ta ajjiye a mazauninshi. Baba Fhatsima tana zaune sai ta dubi Balaraba tausayinta ya kamata. A ranta saita ƙudurce zata tuntuɓi Tasi'u da batun Balaraba ko Allah zaisa a dace yaji ya amince zai aureta a karo na biyu. Dan Balaraba yarinyace mai hankali sosai, kuma bata da wata makusa da za a ƙita dominta. "Altine gobe Balaraba ba zata biki ba. In zaki tafi ita ki barmun ita. Akwai tunanin da nake yi ne. In hakan ya tabbata zaki ji, amman ki barmun ita gaskiya. Daga Balaraba har Altine wani daɗine ya lulluɓesu dukkansu sun gane inda ita Baba Fhatsiman ta dosa. Kuma shi kanshi Tasi'u ya nuna kamar har gobe yana jin Balaraba a ranshi. "Shikenan Yaya Balaraba ai taki ce kumfi kusa, gata nan" Dariya Baba Fhatsima tayi tace. "Balaraba ai zaki zauna tare dani ko? Duk da babu sa'anninki a gidan. In yaso dan kar kaɗaici ya dameki ba sai ki koma islamiyya ba?" Balaraba tace. "Zan zauna Baba ba komai ai nanma gidanmu ne" Tana gama faɗar haka ta fice ɗakko abin kwashe shara. "Shikenan Yaya Wallahi naso in ɗakkota in kawota wajenki ko wajen Yaya Dije. Acan gabana in banda kuka da damuwa babu abinda take yi. Kinga nan kuma birnice ai nima zanso tayi aurenta a birni. Inta koma islamiyya zata ƙaru sosai. Sai dai bata ɗebo kata da yawa ba" Baba Fhatsima tace. "To in banda abinki ai da kin kawota. Batun kaya kuma Yayansu zai siya mata a ɗiɗɗinka mata ta samu na cin zawarci. Allah dai ya tabbatar mana da Alkhairi. Kije ku duba abincinnan fa ko ya nuna. Kwanciya nake son inyi ko ina ciwo yake yi mun an sha kacaniyar biki. Da kuke_koken yara" Ta bangaren Angwaye kuma, suna ɗakinsu na samartaka suna zubar da zance gami da tsokanar juna. Gwadabe dai Baya cewa uffan sai murmushi, jiya ya ƙara tabbatarwa cewar Iyabo na da wata baiwa da ba ko wacce mace bace zata iya samu ba. Rabuwarshi da Iyabo sai ya sake dawo mishi ɗanye. Har ya gama haɗa ƴan kayanshi da basu shige kala shida, da jakar magungunanshi baice komai ba. Bara'u kuwa ya ƙura mishi idanu yana nazartarshi, tuni ya bugo kuwa jirgin nashi, abotar wasan ƙasa ba abota bace ta wasa. ( Fatima Abdullahi Owuna zanso ace kina karatun littafin Hausa, da a daidai wajennan zaki tuno lokacin muna yara). Hannun Gwadabe Bara'u ya ja zuwa waje, Tamu dama baya ɗakin yana wajen Ayashe suna tattaunawa dangane da maganar barin toye da kahinde da Gwadabe yayi musu. "Gwadabe wai shin duk zuƙa_zuƙan matannan kana nufin basu isa sun maye maka gurbin Iyabo bane? Ya kai da kake da Amare kana tunanin matar da ba mallakin ka ba. Babu mamaki Iyabo tana gidan wannan wan nata Debisi tana aurenta cikin kwanciyar hankali tama rufe shafinka, ta shimfiɗa sabuwar rayuwa. Matar da ko yaranta bata sake waiwaya ba shekara biyu fa." "Sabida kasan naƙi jinin Debisi shine ma dalilinka na danganta Iyabo da aurenshi" Da gaske sai gabaki ɗaya ya hautsine. Bara'u kuwa mai zaiyi ba Dariya ba. Dole shima Gwadaben ya dara, tare da dorawa da faɗin. "Kana ji. Aishi tunanin Iyabo tamkar numfashina yake. Zare tunaninta a gangar jikina daidai yake da zare numfashina. Bara'u Iyabo mutum ce harda ɓari kai shaidane kan hakan, kuma ta cancanci a dauwama ana tunanin ta tare da binta da fatan alkhairi. Fatana shine Allah yasa iyakar ƙarshen wahalar rayuwar Iyabo ya ƙare a gidana. ina mata fatan samun mijin da zai kula da'ita fiye da kima. Kai dai mu ture batun Iyabo mu dawo batun yara. Bara'u." "Dakata malam dallah. Nina faɗa maka gaskiyar abinda yafi dacewa. Ka zauna da matanka a nutse ka gama gane kansu tukunna. Toye saiya gama firamare zai dawo hannunka zancan gaskiya kenan. Zuwa lokacin suma ko wacce da nata. Da yazo saiya faɗa sakandare kai mun wannan alfarmar." Dariya Gwadabe yayi yace. "To Shikenan hakan za ayi duk yadda kuka ce. Shi Tamu yama ƙi yadda zai bani yaran. Naga Toye da Husna sunyi wani irin shaƙuwar data haure misali, ko hakan hujjane. Babu komai in suma sai sun gama firamare ɗin za a bani su duk babu komai" Ana haka sai ga Tamu ya shigo ɓarayin. "Me ake tattaunawa aka wani ja gefe?" Cewar Tamu. Bara'u kuuwa yace. "Maganar Iyabo muke yi daka ganmu" Ƙarasowa yayi kusa dasu yace. "Baiwar Allah. Alkhairan Allah ya kai mata a dukkan inda take. Kai kuma Gwadabe Allah ya baka haƙurin rashinta. In sha Allah nan ba da jimawa ba Toye da Kahinde zasu maye maka gurbin Iyabo a zuchiyarka ta ɓangaren soyayya. Amman Ayashe ta ba da shawarar ka ɗan ƙara haƙuri yaran su sake girma ta yanda za a iya morarsu sai mu dawo dasu. Kafinnan sun samu ƴan uwa ma dayawa su kansu sai sunfi sakewa" Haka dai wunin na yau shima ya mutu murus. Sai zuwa bayan ishane Gwadabe ya samu suka shigo cikin gidan. A ɗakin Hadiza suka ya da zanzo. Ɗakin yasha gyara sai ƙamshin turaren wutan Sandal yake yi. Ita kuma tana kitchen tana ƙoƙarin ƙarashe girkin dare. Kitchen ɗin Gwadabe ya bita bata san yana tsaye yana ƙarema ado da kwalliyarta kallo ba. Ɗagowar da zata yi zata buɗe kula babba danta zubo abincin harda su Bara'u carab sai suka haɗa idanu. A take suka sakarma juna murmushin so, Gwadabe harda lumshe idanu dan wani maganaɗisu ke ɗibarshi. Shi Allahn da yayi shi ya kasance mai son mace mai kwalliya da ado, uwa uba son ƙamshi. Kuma ya lura matan maraɗi ba baya ba wajen iya Ado. "Sai yanzu kuka samu shigowa?" Ta tambayeshi cikin kulawa. Da kulawar shima yace. "Muna kofar gidan tun yamma, gidanne cike dam da mata abinda ya hanamu shigowar kenan. Su Auwala duk tare muka shigo. Ba a kawo abinci daga cikin gida bane naga kina girki?" "An kawo tuwon ɓula su ka yi ne, tunda naga kana da baƙi shine nace bari in dafa shinkafa fara da maka, tunda ina da miya sai ku haɗa. " Abincin ta zuba ta haɗa plate da cokula, ga ruwa a babban jug me kofuna shida. Gwadabe ne ya taimaka mata wajen shigar da kayan abincin..". "Hadiza ki yi mun kiran Shafa tazo mu haɗu aci abincin. In aka kammala sai mu ɗanyi muku nasiha" Jimm Hadiza tayi, ba ta dai ce komai ba, can sai tace.." "Ina ganin kai yafi cancanta kaje ka kirata. Tunda rabonnu da kai tun safe" Bara'u daya cusa nama a baki yace. "Nima abinda zance mishi kenan uwar gida. Kuma ko babu komai akwai iyaye a ɗakin a gaggaisa" Miƙewa Gwadabe yayi ya fice. Hadiza tabi bayanshi da kallo. Ji take yi tamkar zuchiyarta bafa zata iya jure zaman kishi ba. Su Bara'u suna ɗan janta da hira dan hila. Amman taƙi hilatuwa hankalinta na bakin ƙofa taga a yaya zasu shigo. Ga abinci ta zuba ita da Gwadabe ta saka cokula biyu. Shi yana gaba ita kuma tana bayanshi. Saye da materiyal ɗinkin riga da siket wuyan rigar kuma faralas ne. Sai mayafinta da babu ta inda ya dace da shigarta. A ƙasa ta zauna kamar yadda taga Hadiza a ƙasa. Ganin abinci a gaban Hadiza sai Gwadabe shima ya zauna a ƙasa kusa da Hadiza sai ya zamana shi da'ita suna fuskantar Shafa. Mrs Bukhari Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 15 "Yaya Bara'u ina wuninku? Yaya barka da dare ya akaji da taro?" Sai lokacin Hadiza ta fahimci ashe lalacewa tayi wajen kallon Shafa, yanda take wani gwalangwaso kamar babu ƙashi a jikinta. Sai da ta sauke ajjiyar zuchiya kafin tace. "Taro alhamdulillah, ya baƙunta,?" Murmushi tayi gajere kawai. Shi kuma gogan sai yace. "Matso ga abinci muci tare. Hadiza bata cokali" Dole ƙanwar naƙi kenan. Haka Hadiza ta ɗakko cokalin ta miƙa ma Shafa. Sai jujjuya shinkafar take yi ta kasa kai ko loma bakinta. Shafa da Gwadabe kuwa bil haƙƙi suke cin abincinsu. Carab a idanun Hadiza suka sakarma da juna wani murmushin ƙauna wanda ya kusan tarwatsa kan Hadiza. Shigowar Auwala da Amaryarshi Shatu, da Mammada da Amaryarshi Nana ne ya sanya Hadiza ta ɗago da fara,'arta ta tarbesu. Matan a ƙasa suka zauna, Mammada da Auwala kuma suka zauna a sama. "Amare kun sha ƙamshi, kun rigamu shigowa naso in shiga da yamma to na ɗan tsaya yin gyare gyarene. Bari a zubo abinci ko?" Auwala da yasa hannu a abincinsu Bara'u ya soma ci yace. "Yauwa dama Shatu taƙi cin tuwon ɓula wai ita shinkafa zata ci. Dama naso daga nan in kaita ɗakin Anty Badi'a ne nasan zamu samu abinci. Mammada zo mu muci nan. Hadiza ƙaro mana" Ya miƙa ma hadiza tiran abincin ta zuba musu. Nan ta zuba ma Amaren Yayun nata. Gwadabe da Shafa sai abincinsu suke ci, anata nishaɗi. Su Shatu ma suka saki jikinsu suka ci abinci. Hadiza fa sam taƙi cin abincin da wayo_da wayo. Bayan duk an kammala cin abincin sai su Bara'u suka haɗe nasihar da zasu yi musu du harda matan su Auwala. Daga haka kuma suka yi ma Hadiza Sallama, tare suka fita dasu Auwala da matansu zasu kaisu ɗakin Yaya Tasi'u da Yaya Jamilu. Ɗakin ya rage daga Gwadabe sai matanshi. Tattare kwanuka Hadiza ta soma yi. "Zauna Hadiza inaso in ɗan yi magana daku nima" A sanyaye ta ajjiye kwanukan ta zauna a ƙasa shi kuma yana bisa kujera. "Da farko dai ina mai roƙonku arziki ku haɗe kai ku samar da farin ciki, nutsuwa, zuriya ta gari a gidannan. Dole ku haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen haɗe kawunanku. Kar ku bari wasu su shiga rayuwarku su yi ƙoƙarin tarwatsaku. Gidannan cike yake da facaloli ke Hadiza kinsan komai. Nima ina da ilimi akan irin zaman, ni da Iyabo mun zauna tare da su Yaya Hambali, babu irin gulme_gulmen da ba'ayi a tsakankanin mata. Ni bazan hanaku tsaɓin kawaye a cikinsu ba, amman na horeku da ku iya bakunanku. Duk da dai ku ba mazauna bane, ke kina aikinki na koyarwa itama Shafa Yaya Tasi'u ma yace ta bashi takaddunta zuwa gobe in aka nutsa zan kai mishi zai samar mata aiki. Dan Allah ku taimaki talakan mijinku ku bashi nutsuwa, aikina na wahalar gaske ce ina roƙonku da ku samar da farin ciki a gidannan. Ni in so samune yau in ganku a wannan ɗakin gobe in ganku a ɗakin Shafa kuna hira kuna dariya." Fasali yaja tare da ɗan yin murmushi, suma murmushin suka mayar mishi. "To kasancewar gobe zan bar ɗakin uwargida, kamar yadda addini ya tanadarma matar data taɓa aure inta kuma wani aure kuma tana da kishiya kwana uku Shari'a ta tanadar mata. Hadiza a matsayinki na babba da kwanan da rabon girkin na baki wuƙa da naman faɗin yadda za'ayi, kuma in sha Allah yadda kika ce hakan za'ayi" Hadiza wacce ƙwalla ta taru a idanunta tun lokacin da Gwadabe ya kirata bazawarar data taɓa aure a gaban kishiyarta, kuma ta ɗauki hakan a matsayin tozarci. Ta ɗanyi yaƙe tace. "Nagode da wannan girma daka bani. A babin maslaha ina ganin tunda du mu biyun masu fita aikine zaifi kyau ace ko wacce ta dinga girkinta kawai, gudun shiga hakkin wani. Dangane da rabon kwana kuma ayi kwana uku_uku. Sannan ni na baka damar shiga ɗakin Amarya a darennan kwanana guda ɗaya na yafe shi naci girma." Tsam Gwadabe yayi yana karantar yanayinta da duk ya sauya, ya riga yasan da Hadiza zai samu matsala kishinta yayi yawa. Yanata tunanin to meye abunda ya ɓata ranta yanzu_yanzu. Kawar da tunanin yayi da cewa. "Ba za'ayi haka ba, kuma ai akwai danginta a ɗakin sai zuwa gobe zasu kama hanya. Dangane da rabon girki da kwana naji abinda kika ce, kuma dama nayi miki alƙawarin duk yadda kikace ta zauna. Inaga in kuna da wani ƙarin bayani zaku iyayi" Du su biyun suka ce basu da wani ƙarin bayani. Sallamar Shafa yayi ta koma ɗakinta. Hadiza kuma rai a murtuke take ta faman kai kawo na fitar da kwanukan da aka gama cin abinci. Ruwan wanka ta kai mishi harda ɗiga mishi wannan haɗaɗɗen turaren wankan data siya a hannun mai gayya mai aiki Mrs Bukhari ( kema ki mallaki naki yana da sirri) "Na kai maka ruwan wanka kaje ka watsa" A madadin ya tashi sai ma ya riƙo hannunta yai mata masauki a cinyoyinshi, dan nauyi sai da ƙashin guiwarshi yayi motsi mai zafi. Shi ya ƙura mata idanu, ita kuma ta ƙurama ledar tsakar ɗakinta idanu. Can sai hawaye shar_shar suka soma zubo mata. "Ya Allah Hadiza menene ya kawo kuka kuma, shin nayi wata maganar data sosa miki ranki ne?" Shiru tayi shima shiru yayi yana kallonta da dai yaga abun bana ƙare bane sai ya rungume abarshi yaima bakinta riƙon alawar yara. Ji kake shiru sai sautin ajjiyar zuchiyar Hadiza. Sun jima a cikin wannan koramar da kyar ya zare jikinshi a nata. Miƙewa tayi da sauri, yai mata dariya tare da girgiza kai. "Ke ba yarinya ba, amman kinfi yarinya shagwaɓa bari in fito wanka sai kin faɗamun sanadin zub da hawayennan kina Amarya" Dariya tayi kawai. Shi ya wuce wanka ita kuma ta wanke kwanukan da akaci abincin a ƙaton bawo a kusa da kitchen ɗinta. Tana ganin shige da ficen Dangin Shafa. Yaya Tasi'u ne yazo wucewa. "Yaya Tasi'u sannu da dawowa" kallonta yayi yana dariya. Hannayenshi rike da ledoji kawai saiya miƙo mata leda ɗaya. "Zo ki karɓa Hadiza rabonku ne dan tunda na shigo gidan banci karo da kowa ba" Da sauri taje ta amshi ledar tana murna tare da yi mishi godiya. "Ina Gwadaben?" "Wanka yake yi, ni kuma wanke_wanke na gama" Kafin ya bata amsa Yaya Jamilu ya shigo gidan shima. Abun mamaki wucesu yayi ba tare da yayi musu sallama ba balle ya tsaya a gaisa, ɗauke kanshi yayi kamar ma bai gansu tsaye ba. Tasi'u ya girgiza kai yace. "Allah ya nuna mana lokacin da iyalan Malam zasu haɗe kawunansu su mayar da damuwar ƴan uwansu damuwarsu. Sai da Baba ta faɗa dama haɗakaarnan babu abinda zata haifar face sabon rikici. Jafaru da matarshi ne suka fito daga ɗakin Zangina, sai fa da suka zo dab damu Jafarun yace. "Sannunku" Itako matar tashi kalloma basu isheta ba" Kasa amsawa dukkansu suka yi suka bisu da idanu har saida suka shige ciki. "Jeki ciki Hadiza kinji. Allah ya bamu lafiya sai da safe" Jiki a mace Hadiza ta shige ciki. Lemo da ayaba ne a cikin ledar da Yaya Tasi'u ya bata. Lemun ta yanka musu ta saka a plate, Gwadabe na shigowa falon ƙamshin turaren wankan data zuba mai ya daki hancinta. "Ina kuma muka samu lemo?" Yai mata tambayar yana mai ƙureta da ido. "Yaya Tasi'u ne ya bani. Haɗuwa muka yi shi zai shige ɓarayinsu, yace a gaisheka" "Ayya ina amsawa." Wanka Hadiza tayo itama, a daren Gwadabe ya mantar da'ita wata damuwa data ɗaurama kanta. Washe gari kuma Dangin Shafa Amarya da su Goggo Iyatu duk suka ɗunguma suka kama hanyar Takai, su Goggo Iyatu ko sallama ba sui da Gwadabe ba balle Amaren shi. Sai su Sakina da Ayashe ne kawai suka shigo su kai sallama da Hadiza. Gidan ya gare daga sabbin Amaren sai su Yaya Tasi'u. Tun bayan tafiyar ƴan Takai Shafa ta shiga aikin gyaran ɓarayinta, daga cikin uwar ɗaki zuwa falo, zuwa kitchen. Daga cikin gida yauma aka kawo musu abincin karin kumallo. Tun bayan data ga Gwadabe yayi ma su Bara'u rakiya zuwa tasha, bata sake sanyashi a idanunta ba har azahar. Tana zaune tana cin nakiya tana kurɓar shayi sai gashi ya shigo da fara'a ɗauke a fuskarshi. "Amarya bakya laifi daɗi ake ci ne?" Murmushi tayi mishi kafin tace. "Kaga nakiya ce nake ci na ɗan soma jin yinwa" Zama yayi a kusa daf da'ita ya gutsiri nakiyar ya jefa a bakinshi. Yana ƙarema ɗakin kallo yanda ta sake mai fasali yafi na farko fiye. "Me yasa baki ɓararraka ko taliya bace, ba naga taliyar Hausa a kitchen kusan kwalla uku ba, ai ko mai da yaji sai ki zuba. Tunda su Baba Fhatsima sunma yi ƙoƙari suma suna buƙatar hutu. Naji gidan duk ya kaure da ƙamshi da halama amaren gidan sun soma girki" Sailuba ɗiyar Yaya Tasi'u ce tayo sallama ta shigo. Hannunta riƙe da filas ɗin abinci, a gabansu ta dire tare da gaishesu cikin girmamawa. "Innata ce tace in kawo. Tace kiyi haƙuri aikine yai mata yawa sai yanzu ta sauke sanwar" Murmushi Shafa tayi tace. "Babu komai kice mata nagode Allah ya saka da Alkhairi" Da "Ameen" Sailuba ta amsa tai musu sallama ta fice.Shafa kuma tayi sauri ta ɗakko plate da cokula biyu ta juye musu abincin. "Bismillah mu ci ko tunda dai kana nan aka shigo da abincin " Bai mata musu ba sai yayi kamar yadda tace dashi. Hadiza kuma tana can ta tusa abinci a gaba tana jiran shigowar Gwadabe su ci, yace zai ɗan leƙa Shafa a tsaitsaye. Yau zai shigo, gobe xai shigo, saida ya share awa uku kyawawa. A wannan lokacin Hadiza ta kai maƙura wajen ɓacin rai. Abincinta ta zuba tayi shigewarta ɗaki ta zauna kenan akan gado ta jiyo yana sallama a falo. Jin motsin cokali a uwar ɗakine yasa ya leƙo uwar ɗakin suka haɗa idanu, take yasha jinin jikinshi, amman lokacin sallah ya riga da yayi haka dole yayi alwala ya tafi masallaci. Yana dawowa kuma kamata yayi ya ɗebi ƴan suturu ko kala ukune ya koma ɗakin Shafa daga la'asar kwananta zai soma. Har ya gama ɗiban kayan da zaiyi amfani dashi Hadiza tana daga kwance tana kallonshi, sai tubka da warwara take yi. Wani irin muƙu_,muƙun kishi ke turniƙeta. A kusa da kanta dab ya zauna yana shafar sumar kanta dake sheƙi da ƙamshi. "To ni kam zan tafi Hadiza. Sai bayan kwana bakwai zan dawo. Zanyi kewarki sosai, tare da wannan ƙamshin naki mai tasiri a zuchiya" Wani kallo tayi mai shi ba harara ba, shi ba kallon so ba. Dan ya kasa fassara irin kallon.. "Abincinka dake ajjiye a falo fa, kaci ne?" "A'a ɗazu ina shiga ɗakin Shafa Sailuba na kawo abinci. To shine shafar ta zuba mana, kinga ai ba zata ji daɗi ba in banci ba, kafin zuwan Sailuba kuma naci nakiya" "Agen? Hmmm shikenan a sauka lafiya ango. Lallai ga zumuɗin yage tantani nan ina gani a tattare da kai. Nutsuwarka harta gushe sabida kula da kai zai koma hannun Shafa " Baki ya buɗe zai yi rarrashi. Tayi saurin ɗaga mishi hannu, sai kuma ta fashe da kuka. Ƙur yayi yana kallonta kawai yana tunanin irin danƙareren aikin dake gabanshi. Dan ya lura Hadiza bats son a zauna lafiya balle a samu haɗin kan da zai samar da nagartattun ƴaƴa. Da wuri ya kamata yaima tubkar hanci dan gudu kada wankin hula ya kaishi ga dare. Masu iya zance na cewa. Itace tun yana ɗanye ake tankwarashi, matsawar ya bushe to sai dai a ɓallashi. Dannewa yayi ya shiga aikin rarrashinta da shafar bayanta har tayi shiru. Tana gani ya fice a ɗakin Izuwa ɗakin Shafa. Tohfa MRS BUKHARI 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 16 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 IYABO:. Lalubo lambar Yaya Hamma nayi a wayar Faty na danna kira. Nan take zuchiyata ta shiga harbawa fafafat, ina jiyo motsin sonshi a zuchiyata. ( M Farida Ana magana )Sau uku ina gwadawa number bata ma shiga, kamar ma layin a ƙasa yake baya cikin waya. haka dole na haƙura, na bari zuwa wayewar gari, in sake jarabawa ko Allah zaisa in dace. Bacci a ranar lafiyayye muka samu mai nutsuwa. Bayan munyi sallar asuba ma bacci muka sake komawa ba mu muka tashi daga baccinnan ba sai azahar, ni dai akwai gajiya marar adadi tattare dani, haka ma Uwani. Faty kuma dama ita ɗabi'ar baccinta kenan. Alwala muka ɗauro bayan duk munyi wanka. Kayan jikinmu muka mayar dan kayanmu na cikin mots ba'a sakko dashi ba. Ina sallah Salim ya shigo, abinci ya kawo mana da burosai na goge baki da makilin. Kafin in idar ya fice. Ina idarwa ya sake shigowa da wata zungureriyar leda shaƙe da dogayen riguna da takalma harda agogo, da tarkacen kayan kwalliyan mata harda turare. Ya miƙo mini, nasa hannu na karɓa ina mai mishi godiya. Sai cewa yayi dani da harshen larabci. "Ki shirya zan gabatar dake a wajen dangina. Kakata ma tana nan sai su ganki" Na dubeshi, sai yayi mun murmushi. "Tuni labarinki duk ya karaɗe familyna. Na faɗa miki sonki nake yi da aure ba da shashsnci ba. Tun rabuwar dake zuchiyata bata huta ba wajen begenki da mafarkin mallakarki" Ya sake faɗa. sai na gyaɗa kaina nace mishi. I am coming ( ina zuwa) shiga uwar ɗaki nayi na tarar da Faty tana waya. Uwani a falo na barota. Faty wai ashe da gaske salim yake yi aurena yake so yayi? Kinga fa kaya ya bani wai in saka mu sauka ƙasa zamu gaisa da iyayenshi. Sai ta zare wayar a kunnenta tace. "Kwarai kuwa. Komai a rayuwa yana da sanadinshi. Da kina Najeriya babu dalilin da zaisa ku haɗu da Salim har ya soki, tunda baisan hanyar Najeriya ba." Faty akwai Matsala ne akwai ɗan uwana da mu kai alƙawai dashi kafin in baro ƙasata" Buɗar bakin Uwani wacce shigowarta kenan sai tace. "Akwai dai wanda kika ɗafa sonshi a ranki dai banza. Yanzu haka yama mance dake. Babu mamaki in mutumin ƙauyene kije ki iskeshi da mata huɗu ma, kinga babu wajen zamanki a gidanshi ai. Yanzu kamar wannan bawan Allah yaji sonki kina neman kisa ƙafa kiyi fatali da damarki. Wai Iyabo a ƙauyen ƙayayau ɗinnan kike so kiyi rayuwa, kina ɗaukar tallar nono aka? Ke sha'awar rayuwar kenan kike yi. Koko sabida fari, gashi da tsawon Hamma ke ruɗarki? Duk da dai nasan ba hakan bane tunda Salim ya kere Hamma a komai. Amman dai Iyabo Allah ya wadaran wannan zuchiyar taki ta gaban ƙirjinki" Ta ƙarashe zancan ta tana hararata Turus nayi ina kallo da sauraren Uwani da take ta balbalin faɗa kamar Uwata. Faty ce ta katse hirar da cewa. "Yanzu dai ki shirya kije ki dawo mayi magana. Uwani mu karya kafin ta dawo" Ni dai a tsorace du nake. Doguwar baƙar riga na saka mai shegen kyau, da takalmina baƙi mai tsini, na yane kaina da mayafin rigar tare da feshe jikina da wani turare mai ruwa ja. A tsaye a inda na barshi na sameshi. Ba sai mutuminku ya nemi lalacewa dan kallona ba. Ni kuma sai kunya ta kamani a raina sai nake ayyana. Wannan kallo da yake yi mun kallon yaudarace kawai, su da suke da haske da kyau, matansu Allah ya basu diri da cikar ƙirji. To ni meye a jikina na kallo da har za'a shagala in ba ɓaka_ɓakan mazaunai ba? Ashe shi yasan dalilin, tare da larabawa masu auren ɓaƙaƙen fata, da turawa masu auren baƙaƙe su bar kyawawan fararen matansu. Haka muka gangara a jere muka tadda ahalin gidan a daining table babba suna cin abinci. Da ganina wata tsohuwa ta iso inda muke ta riƙo hannuna har gaban daining ɗin. Zaunar dani tayi a kujerar kusa da wani tsoho. Shima Salim ya samu waje ya zauna. Jikina yana ɓari na gaishesu da larabcina irin nami na ƴan koyo. Da soyayya gami da fara a suka amsa mun. Ya dinga nuna mun ƴan uwanshi, yayye da ƙannenshi. Ga mahaifiyarshi da mahaifinshi, sai kakarshi da mijinta, sai kuma Yarshi Sarla da mijinta Umaid. Ni dai duk ina zaune a mugun takure, su kuma sai jana da hira suke yi. Mahaifiyarshi ta tambayeni asalina. Ban ɓoye mata komai ba kama daga yarena, izuwa aure da nayi a baya da adadin yarana. Duk da haka sun yi na'am dani. Abu guda dana fahimta da larabawa ko basason abu. Muddin yaransu ya nuna Yana so, to suma zasu koyi son wannan abun. Suna da son yara, su kuma yaran sai suke Amfani da hakan wajen tursasama iyayen son ra'ayinsu da yarda dashi. Gurasa da nono aka zuba mun sai shayi, a kunyace na ɗan cakala Salim yace in tashi ya mayar dani. Sai mahaifiyarshi tace ba za'a yi haka ba. Ya ɗaukemu daga ɗakinshi ya dawo damu wani ɗaki dake kusa da nata, ɗakin ƙanwarshi dake karatu a landan. Haka kuwa akayi, ɗakin yafi nashi kyau da kuma yalwa. "Ku shirya zuwa dare sai mu fita daku kuyi siyayya, ku ga gari kuma." Cewar Salim bayan mun samu keɓewa nake sanar mishi ni Najeriya muke son komawa, zaman bautar da muke yi ya ishemu. Anan yai mana alƙawarin zaiyi mana cuku_cukun visar da zamu koma, zaima biya mana, amman in mishi alƙawarin zan bashi damar kafa soyayyarshi a zuchiyata dan shi da gaske aurena yake son yi. Tuni na amince mishi da hakan magana ta domin Allah ba har cikin zuchiyata ba amma. Da daddare ya fita damu zuwa wani super maket babban gaske na suturu masu tsada da masu arha duk gasu nan. Mu ka dai tsittsinci abinda ba a rasa ba haka. Ya biya komai muka sake nausawa zuwa zagayen cikin gari. Ni dai banyi ƙumun baki ba nace mishi ni kam inason yin Umara. Ranar juma'a yai alƙawarin zai kaimu da izinin Allah. Ai kuwa hakan akayi. Daga umara muka shiga kasuwar DOGON GIDA dake Makka. Anan muka ga dandazon maza da mata na Najeriya iri iri. Ga gumama a zube a ƙasa, ga sababbi, zannuwan gadone, takalma. Komai da komai dai. Nan Faty ta dinga kutsawa damu. Siyan kaya muka dingayi. Ni da Uwani mune harda maƙala haƙori makka bibiyu a bakunanmu. Adai taƙaice mun kaso kuɗi masu yawa, daga haka muka koma Jidda, nanma suna da babbar kasuwa Faty ta kaimu, ni har dilar zanin gado, da kayan mata dogayen riguna da takalma na siya za a ɗauro mun a jirgin kaya. Ɓangaren kayan kitchen hatta plate da cokali saida na siya, na sai manyan kuloli kala biyu, masu filas na shayi. Uwani kuma dila biyu na zannuwan gado da dilar Kayan sawan yara ta siya. Daddumai, da carbi, bagaruwa, dabino, ruwan zamzam kuwa sunfi komai yawa a tsarabarmu. Naima Dada tata tsarabar, naima Iyaa Debisi nata daban, naima Yaya Hamma nashi daban shima. Su Boɗɗo kuma saina isa Najeriya zansan mai Zan cire musu dai, ragowar kuɗaɗen muka canjasu zuwa kuɗinmu na Najeriya.. Duk wannan siye_siyen da taimakon Salim, da taimakon mahaifiyarshi danta bani kuɗi a gaskiya masu kauri. Suna da wani irin karamcin da a ɗan kwanakinmu a gidan Salim harya soma samun gurbin zama a zuchiyata. Kwananmu takwas a gidansu Salim Allah ya kawo lokacin dawowarmu Najeriya, mahaifiyarshi da danginshi su kai mana goma sha tara na arziki, har zoben gwal yarshi Sarla ta bani ɗan ƙarami na maƙalashi a hannuna. Duk tarin kayayyakinmu mun ɗaure zasu tawo a jirgin kaya wanda akace bazai wuce wata ɗaya ba zai iso. Sai ƴan akwati da jakunnanan kaya, da jakar hannu kawai muka riƙe. Har filin jirgi Faty ta rakamu, Salim shima yana wajen tare da Yarshi. Sai sake jaddadamun yake yi akan in riƙe mishi alƙawari, sannan zai biyo adireshin gidanmu na Kano dana bashi yazo a kawoshi har ƙauyanmu nanda sati biyu in ya rage abubbuwan dake gabanshi. Sarla itama sai sake roƙona take yi akan kar in yaudaran mata ɗan uwanta. Zai zo da kanshi neman aurena. Ni dai duk sai jikina yayi sanyi tuɓis, har na soma kokonton wanda zan ɗauka da wanda zan ajjiye. ( To masu karatu wannan zaɓi ayi daku. Ku wa kuke ganin ya cancanta Iyabo ta ɗauka Hamma ko Salim?) "To Faty Allah ya sada fuskokinmu da Alkhairi. Zamu dinga waya in sha Allah. Da haka mu kai sallama da juna. Muna hawayen farin cikin komawarmu ƙasarmu Najeriya. Faty tana kukan sabo, Salim da Sarla suna cikin alhini da fargabar kar in yaudaresu. Da misalin ƙarfe Taran safiyar ranar laraba jirginmu ya tashi daga king Abdulaziz Airport jidda. Tafiyar awa biyar da minti hamsin da biyar ce ta sauke mu a Airport na Legos Murtala Muhammad. Kai tsaye daga Airport muka wuce tasha. Wata sassanyar iskar ƴanci na kaɗamu zuchiyoyinmu cike da farin ciki marar adadin kwatance. Tiket muka siya, motarmu sai ƙarfe biyar na yamma zata tashi tafiyar ta dare ce. Masallaci muka samu mu kai Sallah. Uwani muje mu nemi abinci mu ci yinwa kamar zata kasheni" Na faɗa ina riƙe cikina. Wani ɗan ƙaramin gidan cin abinci muka shiga. Abinda suke siyarwa tuwon eba da miyar ganye, sai sakwara da miyar egusi. Sakwarar muka siya da nama gunduna_gunduma. Muka ci mu kai ƙat, kana muka koma masallaci, mun bar motar da zamu shiga anata lodin kaya. Bayan la'asar muka shisshiga mota kowa ya zauna a muhallin zamanshi. Gaga_gaga sai gamu a Kano ta dabo tumbin giwa ko da me kazo an fika da misalin ƙarfe shiddan Asuba, garin da duhunshi a lokacin. A tasha muka sallaci asuba. Uwani gidanki kika nufa ko gidan Hajiya?" "Gidan Hajiya dai zanje, in yaso shi Hafizun yazo ya sameni a gidan, zan aika Habu ya nemoshi" Mota muka shiga har zuwa bakin layinmu. Muna sauka sai gamu ga Lekan da abokinshi suna atisaye. A guje Lekan ya karaso. "Ahh Antimi Iyabo. Okaabo" Farin cikine ya lulluɓeni marar adadi. Jakunkunanmu suka kinkima, abokin Lekan yabi Uwani, ni kuma Lekan ya bini. A kofar gida muka samu Iyaa Debisi tana shara, ga shago harta buɗe. Ɗagowar da zata yi muka haɗa idanu. Saina fashe da kukan farin ciki dan ada na fitar da ran sake sanyasu ga idanuna. Iyaa ai saita soma wannan kwakwazo data saba, kafin kwabo jama'ar gidanmu duk suka firfito ciki harda yemisi da titsetsen cikinta a gaba, ko me take yi a gida duku_duku ohon mata dai. Iyaa Kokodeen ce ta ja hannuna zuwa cikin gida ɗakin Iyaa. Nan aka shiga gaisawa da tambayar bayan rabuwa. Sai cewa suke yi nayi kyau na yi haske, amman na rame. Ni dai sai dariyar yaƙe. Ruwan wanka Lekan ya kaimun, na shiga na gargasa jikina. Kafin in fito nazo na tarar da kwanukan abinci har daga maƙota. Sannan matan unguwa har sun soma cika gidan anzo yimun sannu da zuwa. Na zama kamar watan ramadan, kowa sha'awata yake yi haƙorina na maka har biyu maƙale a bakina sunata sheƙi, na fahimci hakan ya ƙaramun kwarjini sosai. Ni dai sai yaƙe baki nake yi, amman ta ciki na ciki. Amala naci na ƙoshi na sha baƙin bunu. Kwanciya nayi dan in ɗan huta, dan a niyyata gobe in Allah ya nuna mana zan kama hanyar ƙauyanmu, suma in gansu su ganni, sannan inga ajiyata dana ajjiye.( Maƙiyan Hamma ya jiki? 🤣) Bani na farka ba sai azahar, Burodami Debisi da Burodi Kokodeen suna ɗakin, ga yemisi a gefe ana musu sulhun da aka saba. Burodi Debisi muna haɗa idanu yayi mun murmushin da ada in banyi mafarkin irinshi daga gareshi ba yau, nayi gobe dan tsananin yadda nake mafarkin in zama matarshi. Sai gashi kash yanzu idanunshi a kulle suke akan sona. Yayinda nima idanuna suka makance akan son Yaya Hamma. "Iyabo kece kika sake wani kyau da kwarjini haka? Kai maraba lale da shigowa ƙasarmu me albarka." Kaina na sunkuyar dan bazan iya juran irin muguwar hararar da yemisi ke watso mun ba. Kafin in gaishesu Yemisi tace. "Dama a wannan karon ke kike barazanar kashe mun aurena sai gashi kuma kin dawo gida. Dan Allah in aurenshi kikeso kiyi me yasa tun farko ba kui aurenba, me yasa zaki ɗauke tunanin mijina daga gareni" " Mama Iyare Yemisi ( Kinci uwaki Yemisi)" Iyaa ta zageta, dama dai jira take yi sai ta sau kuka kawai. Ni kuma so nake in yaɓa mata maganar da zata sake ingizata amman saina gaishe da Burodami Debisi, da Burodami Kokodeen, Kokodeen yace. "Tunda kika tafi ba'a waya dake. Iyaa har ramewa tayi sabida tunanin ko kina lafiya. Hakama Dada da wani dogon ɗan uwanku Hamma. Dan duk sanda Dada zata zo tare suke zuwa, suna yawan zuwa in banda kwana biyunnan da basu zo ba muke tunanin ko ba lafiya ba.. Gabana ya yanke ya faɗi ras jin an ambaci ba lafiya ba. Yanayin aikine, kuma ni bama waya a hannuna shiyasa. Gobe sassafe nake so dama in wuce Jeren." Burodami Debisi yace. "Ki zauna ki huta mana kafin ki tafi" Iyaa tace. "Gara taje, ina tunanin Daso ko babu lafiya fa. Wannan karon sun jima basu shigo ba . Gobe ta kama hanya kawai. Ki yi sallah sai mu tattaka mu je gidansu Uwani kafin Hajiyarta ta rigamu zuwa aji kunya" To Iyaa" Ina faɗar haka na miƙe na fice ɗauke da buroshi da makilin dake jakata. Bakina na goge na ɗauro alwala na shigo. Dabino da bagaruwa da na jefo a jaka da ruwan zamzam na ƙananun fararen roba na ciro ƙullin nasu Iyaa na ajjiye mata. Ga wannan Iyaa, kayanmu suna jirgin kaya. Ba zasu wuce wata guda ba, dan munyi sare_sare sosai ne" Nan Iyaa ta soma rawa tana shi mun albarka. Ai kuwa wannan dabino sai Iyaa ta shiga aikin kididdibashi ana kasabta harda maƙota ma. Da haka suka ci gaba da shari'ar Yemisi dake gabansu, Iyaa ta lallaɓata tasa Debisi ya bata kuɗin cefane akan da yamma zata koma. Ina Idar da Sallah na saka doguwar jallabiya irin baƙin larabawannan ni da Iyaa muka kama hanyar gidansu Uwani. A hanya ne take sanar mini cewar sunje dubo Yarana dai aka tabbatar musu wai yaran suna Abuja wajen Matar abokin Gwadaben. Ajjiyar zuchiya na sauke nasan ko babu komai zasu samu ilimi. Allah shine masani idaniyata cike take da son ganin Ƴaƴana. Amman nasan ƙila yarannan sai sun girma a kwatanta musu inda nake rayuwa su neme ni. Ina musu fatan samun nasara da dacewa akan dukkan abinda aka ɗaurasu akai. Inma karatu, inma sana'a domin dogaro da kai. Daga su hai mahaifin nasu ina musu adda'ar samun ɗaukaka. Har a ka'aba na yi musu wannan adda'ar na jaddada. Da tulin tunani da misalai muka shiga gidansu Uwani dake cike. Ƙannenta duk sun cika gidan, da yaran kawunta dake aure da yaransu. "Ahh Toyosi yau kune a tafe. Sai kika ga baƙin larabawa sun sauka" Cewar Hajiyan Uwani. Musa wanta yana zaune yana cin bagaruwa Yace. "Kaga Hajiyoyin ƙannenmu Makka kiran Allah, kun sha aikin Hajji da umara har kun gaji, ga sallar juma'a a masallacin ma'aiki arrasul S A W." Na kalli Uwani dake daga cikin ɗaki Hafizu da yaranta suna maƙale da'ita. Ido ta kashe mun, ni kuma nayi dariyar da mu kaɗai muka san fassararta. Ai kuwa Musa ya saki ihu. "Ihuhu jibi haƙorin makka yadda yake ƙyalli a bakunanku. Dan Allah ko umara ku biya mana da ramadana dai mu je" Ni dai sai Dariya nake yi. Hajiya na gaisar na shige ɗakin da Uwani take. Iyaa kuma suka shige ɗakin Hajiya. "Iyabo barkanku da dawowa baƙin larabawa" Zama nayi yaran duk suka rufeni. Safwan na ɗauka ya girma sosai. Hafizu ina yini mun sameku lafiya?" "Lafiya lau sai alkhairi. Kin ganni nafi awa nawa ina lallaɓa ƴar rigimarnan amman haƙona yaƙi kai ga ci" Yaran na kalla nace. Amira kama hannunsu, ga ɗari biyu kuje ku siyi wara kuci ko? Kafin kayanmu su ƙaraso yarana na siya muku kaya masu kyau da tsada. Harda Hafizu a washe baki. Suna fita saina dawo da hankalina kan Hafizu. Ina saurarenka" "Iyabo kinsan kun tafi kun barni akan baifi wata ɗaya nima yayi mun ragowa in tafi Canada ba. An samamun aikin da bamu san wanne iri bane. To ko bayan tafiyarku saida muka fi wata huɗu kafinma muka tafi. Tsaiwa kwatanta azaba da wahalar da matasa ƴan cirani suke sha a ƙasashen waje ɓata bakine Iyabo, abun duk gidogace ruɗune. Shekarata biyu a daddafe na dawo da kuɗin da bai taka kara ya karyaba, banda jinyar jiki dana sha. Dawowata ke da wuya ina zuwa ƙauyenmu sai mahaifiyata take nina mun Farida tace ai an ɗaura aurena da'ita. Kinsan mutanen ƙauye gani suke yi wani kuɗi nayi. Ni kuma a cikin kuɗin da nazo dashi da ƙyar na ƙuƙuta harda bashi na sai ɗan ƙaramin gida mai ɗakuna uku rak. Amarya ta tare a ɗaya, ɗayan nazo wajen Hajiya na karɓi yarana suka tare a ciki, ɗayan kuma na kulle mata a matsayin ɗakinta. Shine fa taƙi fahimtata ca take wai ita in saketa kawai. Yanzu taya zan saki uwar Ƴaƴana uhm Alaja Iyabo ki duba zancena sabida Allah kiyi mun adalci" Jikina yayi murus hankalina sai naji ya tashi. Lallai in har haka ta faru da Uwani. Ni kam ina cikin goma sha biyu. Uwani duk sabida rufin asirinsu ta tafi wannan ƙasa, amman jibi abinda ya biyo baya kafin dawowarta. Ina kuma gani da ko kalmar so Yaya Hamma bai furtamun ba?" Da ƙyar na yakice tunani na sauke ajjiyar zuchiya nace. Shikenan Hafizu zata dawo ɗakinta amman dole sai dare. Sai dai da yamma ni da Ummi zamu zo mu yi mata jere" Baki ya washe yana dariya ya miƙe. Har fa ya kai bakin ƙofa ya dawo. "Alaja Iyabo ni kuwa kayan naku masu isowa har dila nawa ne?" Hararar da Uwani ta zabga mishi ce yasa yayi firgigit ya fice yana dariya" "Kikace zan koma Iyabo? Ni wallahi da naso in haƙura da Hafizu. Duk wannan tatsuniyace fa ya baki ɗan iska marar mutunci" A'a Uwani ki koma kan ƴaƴanki, ki riƙe sana'arki ki kula da kanki da Ƴaƴanki. Ki godema Allah ba mazinaci Hafizu ya zama ba, kuma ki gode Allah baki mallaka mishi dukiyar da kika sha baƙar azaba wajen tarata ba. Yanzu dai ki taso muje mu sai kayan ɗaki na gani a faɗe." Harara ta gallamun. Nayi dariya nace. Zaki bari matarshi ta rainaki ne, ke da kike Hajiya? Uwani kiyi haƙuri dan Allah karma ki nuna ma kishiyarki wai kinji zafin abinda suka aikata miki." "To Shikenan Iyabo. Na ɗauki shawararki. Amman sisina bazan iya kashewa akan Hafizu ko matarshi ba wallahi in tsirara zasu yi yawo sun dade basui ba. Muje ni dalla" Fitowa mu kayi, daidai Iyaa itama ta fito. "Ina zakuje kuma?" Zan raka Uwani ta siyo kayan ɗakine da daddare zata koma gidanta" Hajiya ta taɓe bakinta tace. "Sun gama tata ɓurzar kenan? Ai haƙuri dama dole za,a yi daga ƙarshe, kindai ga halin mazan dai. Wannan ya isheki hankali sai ki tattala dukiyarki kiyi abinda zai fissheku. In da ke kaɗai kike da Hafizu to yanzu ku biyu ne. In da ƴaƴanki ne kaɗai ƴaƴa yanzu suna da Ɗan uba harda wani cikin" Ni dai jikina sake mutuwa murus yayi. Zuchiyata saita shiga cikin taraddadin abinda ni kaina zanje in tarar a ƙauye. Ni dai har muka isa shagon saida kayan katako da Uwani da ƙannenta mata biyu da suketa mana biyayya mu ga hajiyoyi. Kado da sib da mudubi kawai muka siya, sai labule da makeken kafet mai taushi. Kayan kitchen kuwa ɗan tsakura tayi sabida nanda wata ɗaya kayanmu zasu iso. Ni da ƙannenta ne muka wuce gidan, ita kuma ta wuce kasuwar kurmi ɗan siyayyar kayanmu na mata. Gidan wani irin gantalallen gidane ginin laka, ko filasta babu a tsakar gidan, datti da shara takota ina. Hafizun yana zaune a ƙofar ɗakin da ya kasance na Uwani. Amarya kuma sai wanki take yi ga ciki a jikinta ga yaro a ƙofar barandar ɗakinta a kwance." Hafizu masu motar kaya suna waje ka taimaka musu. Amarya barka da gida" Na faɗa a tare. Babu yabo babu fallasa ta gaishemu kana taci gaba da wankinta. Niko ƙare mata kallo na shiga yi tsab, in banda abun ɗa namiji ni dai banga ta inda za'a haɗa Uwani da kishiya irin wannan ba. Ko da yake ita mace duk lalacewarta da ƙauyancinta tana da tata baiwar da Allah ya huwace mata. Dan a hakam saita zama zarah a zuchiyar Hafizu. Shigowar su Hafizu da sib me murfi huɗu ce tasa na dawo hayyacina. Amarya a ara mana tsintsiya dan Allah " Ɗan murmushin yaƙe tayi tace. "Wallahi gidan bani da tsintsiya. Nima da tsumma nake sharar ɗakina" Ai sai na rike baki tsintsiyar laushi ta nera goma ace ta gagari yarinyar mace. Kuɗi na ciro na ba Ummi nace. A siya tsintsiyar laushi data zabori, sai abun kwashe shara, da kwandon shara. Ki siyo kwandon sharar babba da ƙarami, a siyo omo." Nan da nan ummi taje ta siyo dake layin cike yake da shaguna. Tas muka wanke ɗakin muka koro ruwan tsakar gida. Amarya ta bamu tsumma muka goge ɗakin. Muka shirya ɗakin Amarya tas da taimakon Hafizu sai ɓare_ɓare yake yi har ciwo yaji garin shigar da madubi. Amaryarshi sai harara take doka mishi. Ummi nasa ta share tsakar gidan ya dawo saiti, nasa suka wanke ƙazamin banɗakinsu mai zarni da warin masai. Bamu muka bar gidan ba sai biyar na yamma. Zuwa bayan Isha na raka uwani gidanta. Muna shiga ɗakin ta kalli ɗakin ta sharce hawayenta tace. "Iyabo ni kam zan sai gida madaidaici kamar wannan ni da yarana saimu koma. A ɗakinnan ta ina zan soma kasuwanci, banga inda zan ajjiye dilolina in sun ƙaraso ba. Nifa Iyabo haƙurin da zanyi a gidannan na kafin a samamun gidane in siya" Dafata nayi. Uwani babu laifi dan kinyi hakanma. Nima kuma na goyi da bayan ki sai gidan naki ki ware kan ki. Ni zan tafi ƙauye gobe sassafe, in dilarmu ta iso nasan zaki karɓo mana ki ajjiye mun tawa a wajenki. Ni kaina jikina yana bani zanje in tarar Yaya Hamma ya cika gidanshi da Mata, uwani gashi Allah ya jarabceni da tsantsar sonshi. Tsaki tayi tace. "Ni bawai Hamma bai cancanci ki soshi bane. Ni gani nake kashe rayuwarki kawai zakiyi in dai Hamma kike son ki aura. A wannan ƙungurmin ƙauyen kike sha'awar rayuwa alhalin na ƙauye suke fitowa birni Iyabo. Kiyi nazari, ki kuma auna Hamma da Salim, sannan ki yi nazari mai zurfi kafin ki je ki faɗa abinda zai zame miki matsala. Rayuwarki ce kece zaki zauna" Da wannan mu kai sallama na koma gida. Nima da wannan nake cewa daku sai gobe in Allah ya ara mana rayuwar. MRS BUKHARI 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 17 Ina daf da shiga gidan wan mahaifina Alfa Kulle dan in mishi sallamar gobe zan koma ƙauyenmu. Sai naji muryar Burodami Debisi. "Iyabo tun magriba nake jiranki a tsakankanin gidajannan biyu. Dan nasan gobe zaki tafi wajen Hamma. Nayi imani da ace yasan kin dawo da yanzu yana naniƙe dake" Cikin kishi da jin zafi yake maganar. Ni dariya ma ya bani sosai. Sai da na dara tukunna kana nace. To mu shiga inma Alfa sallama in mun fito sai muyi magana. Shi kuma Alfa muna shiga bayan na karanto mishi inaso zan koma ƙauyanmu kamar jirana yake sai yace. "Ba zamu saka miki idanu ba, sai kuma ki kawo maganar aure a gabanki hakanan. Na baki wata biyu ki fito da miji, in baki fitar ba zamu fitar miki. Dan da ace Toye yana da ranshi ma ko Saudiyya da kika je ba zai bari kije ba. Tun kafin jama'a su soma miki wani irin kallo gara ki fitar da mijin aure" Kaina a sauke nace. In sha Allah kafin lokacin yayi zan fitar Baami." A gidan muka ci abinci a cikin ɗakin Iyaa Ramata." "Kin tuna da wancan gadon da in kun mun lefi ke da Bose kuke shigewa?" Cewar Debisi daya samu saken daga ni sai shi a ɗakin. Dariya kawai nayi inacin amala. "Yaya batun aurena dake ya kwana Iyabo? Tunda Allah ya dawo dake ya kamata muyi magana tsayayya" Rai na haɗe nace. Har abada ni da kai ba zamu zama mata da mijiba, muna nan a matsayin Yaya da ƙanwarnan. Na riga na faɗama tun kafin in tafi. Ina ni ina haɗa miji da Soja?" Murmushi yayi mun har yana gyaɗa kai. "Lallai yarinyarnan bakin ki ya buɗe. Nifa wallahi da gaske nake yi, da kinsan irin yadda sonki yake nuƙurƙusar zuchiyata nayi imani da tuni kin ceci ran ɗan uwanki" Kallon dana watso mishi bansan na iyaba, a mafarki banyi zaton zan iya mishi makamancin wannan kallon ba. Amman sai gashi nayi. Hannuna na tsame tsam a abinci na ficewara na bar gidanma baki ɗaya. Koda na shiga Yemisi na zaune tana zaman jiran mijinta su koma gida. Ban jima da shigowa ba sai gashi, ko shigowa baiba cikin ƙailula yace ta fito su tafi, gaga_gaga yai ma Iyaa sallama. "Iyabo wai menene tsakaninki da Hamma? Dan naga damuwar da yayi akan lamarinki abun yayi yawa, yafi ƙarfin ace ƴan uwantakane kawai. Duk sanda Daso zata zo bayan tafiyarki dashi ake zuwa. Shine nake son jin ina fatan ba tallar nono zaki koma yi ba, ki dawo mai sharar kashin shanu da dafa madara. Ai in abune mai daɗi da ba haka ba. Rayuwar matan fulanin daji cike take da bauta, matan da yawa da wannan tallar nonon suke ciyar da gida, su kuma mazan suna bin jeji_jeji suna kiwon shanunsu. Ke irin rayuwar da mahaifiyarki take yi irinta zaki jefa kanki aciki? Kwanaki can da Debisi yaje ya tarar da Daso ba lafiya ga ƙaninki Amaduyal ya dawo daga inda suke fita kula da shanu ga kuɗi a jikinshi a kaita asibiti ubansu ya hana. Sai Debisi ne ya dinga jigilar sai mata magani shima a ɓoye ana bata. Irin rayuwar da kike sha'awa kenan ko?" Illahirin jikina sai naji yana rawa da ƙyar nai kokuwa da harshena wajen sarrafashi. Iyaa ni bazan yi tallar Nono ba. Kuma Hamma shi yana fita aiki a birni masinja ne a ma'aikata bai dogara da iya kiwon shanu ba, mijin Baɗɗo yafi fita da shanun.Sannan.... "Otito ( ya'isa haka) ki dai yi tunani ki kalli uwarki a matsayin mudubi zaki gane mai nake nufi. Rayuwar ƙauye sai ƴan ƙauye madamar suma sun fito ko ziyara dan dole suke zuwa" Ta dinga mun kwatance iri da kala. Da waɗannan tunanin gari ya waye damu. Gaga_ gaga bayan nayi wanka nayi Sallah, saina saɓi akwatina. Nayi sallama da mutan gidanmu sai tasha. Motar Adamawa saura Mutum uku ta cika, nayi zamana ina ta aikin tunanin yadda rayuwa zata kasance inna auri Yaya Hamma. Sai wani shashe na zuchiyata ya tunasar dani cewar "Ai masoyi masoyine imma a birni imma a ƙauye. Zaman aure nutsuwa ake nema, soyayya babu ruwanta da ɗan birni babu ruwanta da ɗan ƙauye. Ban rufekuba na faɗa muku ni Allahn da yayini in inason abu idanuna rufewa yakeyi bana ji ko gani akanshi. ( Ina maƙiyan Hamma kuna dai jin tsuntsun soyayya abinda take faɗe) Wannan tunanin saiya saisaitani, yayinda motarmu ta saitu a hanya ita kuma, mukaita ratata gudu. Bayan gushewar sakanni, mintuna, awanni sai gani a Jere Banyo cikin yardar Ubangiji sai dai galabaita da nayi. Hanyar shigowan tananan inda na barta babu abinda ya canja. Gidan Yafendona na nufa kai tsaye da sallama na shiga. Harira kaɗai matar Jatau ce a gidan itama da halama dawowarta kenan. "Jabu use kece a garin naraba da baƙin larabawa" Da kwaɓaɓɓiyar Hausarta tayi magana Nice Hari, Yafendo bata dawo tallan nono bane?" Sai naga fuskarta ta sauya daga murnar ganina izuwa alhini. "Hmmm Yafendonki tana gidanku wajen Baba Daso jikinta yayi tsanani sosai yau dan ance batasan wanda yake kanta ba ma" Daga tsayen na saki akwatina iyakar jakar hannuna da kuɗaɗena suke ciki na sake mata kyakkyawan riƙo. Sauri_ sauri gudu_gudu na dinga haɗawa dashi zuchiyata tana fat_fat harna iso ƙofar gidan. Dawowar Baffan su Boɗɗo daga kiwo kenan. Yana tsaye yana kora shanu ciki. Ni kuma na rakuɓe a gefe ina jiran garken shanun su gama shiga, mu gaisa in kuma roƙeshi inason ganin Dada. ko kallon inda nake baiyi ba har sai da shanun suka gama shigewa ya kalleni. "Kar ma kice gidannan zaki shiga. Na haramta miki shiga cikin gidannan ɓilgel (Yarinya) Dan haka kiyi maza ki bar wajennan. A guje wani saurayi ya fito yana faɗin "Baffa Dada zata mutu jijjiga take yi" Jin haka yasa na kutsa kai da gudu cikin gidan, da kuma ƙarfina dan idanuna ya rufe sai ganina nayi a ɗakin Dada a tsaye. Baffan yayi yinƙurin hanani shiga gidan, da ƙarfin tsiya na bangajeshi nayi shigewata Tozali nayi da sanyin idanuna yana tallafo kan Dada daga kwancen da take duk ya kiɗime. Wata ajjiyar zuchiya ya sauke. "Adda Jabu ashe kin dawo, gashi inzo kin samu Dada a wani irin mawuyacin hali rai a hannun Allah" Cewar Baɗɗo data ƙarashe maganarta da kuka. Hannunta na riƙe nima ina kuka ƙannena suka tawo gareni suna neman kafaɗar da zasu ɗaura kansu suyi kukansu. Mijin Baɗɗone yace. "Amaduyal dole fa akai Dada asibiti" Inajin haka nace. Anemo mota maza zamu kaita asibiti yanzu" Da sauri na ƙarasa kusa da'ita da ƙyar take jan numfashinta Yaya Hamma yana goge mata fuska da jiƙaƙƙe tsumma dan zazzaɓin jikinta yayi tsanani ainun. Sannu Dada" Carab tana jin muryata Allah cikin ikonshi saita riƙe mayafina carab kamar wacce zata gudu. Kukanmu kawai ke tashi a ɗakin har su Amaduyal suka shigo da sauri Yafendo Mahaifiyar Yaya Hamma tace. "An samu motarne?" "Ansamu malam iro zai kaita a motarshi. Ina fita shi kuma ya kawo kaya yana saukewa," Kintsa Dada akayi bayan mazan sun fita daga ɗakin. Dani da Boɗɗo ne muka tarairayota jikinmu su Yafendo na taimakawa har muka fito. Kishiyoyin Dada su kai ca a kanmu. "Ke Boɗɗo ba Baffanku yace kar a kuskura a fitar da'ita gidan ko wanne me magani ba?" Yafendo tana sharce hawaye tace. "A wannan gaɓar da Yaya Daso take buƙatar taimako, bama buƙatar sahakewar mai nagge. Mujenku Jabu" Har munje bakin ƙofar fita muka jiyo Baffa a bayanmu yana cewa "Indai kuka nuna kun fini iko da Daso, to in kuka fitar da'ita a gidannan to na saketa saki ɗaya. Ku kuma Cubu ku wuce cikin gida ƴan gatan uwa." Wani baƙin cikine ya dirarmun a ƙahon zuchiyata babu shiri na runtse idanuna, yayinda hawaye masu zafi sukaita shatatomun. Amaduyal da Hamma ne suka amshi Dada suka fice da'ita. Yafendona tana kuka tace. "Me nagge kanka ka cutar ba Daso ba. Kuma ka sani sai Allah ya tsayar daku ya fitarma da Daso hakkin zaluntarta da kayi a rayuwa. Ga gidanka nan, ƴaƴanma gaka gasu ƙila sune zasu zama jarabawarka. Sannan ka shirya tsab tunda bakwa aure dole ka dawo mata da garken shanunta." Da gaggawa muka fita a cikin gidan, Yaya Hamma ni yake kallo idanunshi sun zama jawur kamar garwashin wuta. Namadi ne yace. "Yafendo ku shigo mu tafi numfashinta tuni ya ɗauke fa" Bayan akori kurarnan muka shiga dukkanmu. Boɗɗo tana goye da wata fara kyakkyawar yarinya mai gashin fulani a kayinta. Sai dai ita uwar duk kazanta da rashin zama a waje ɗaya ya komaɗar da'ita. Kaina na sauke ƙasa ina ma Dada adda'ar Allah ya bata tsawon rayuwar da zata ji daɗi taci ribar ƴaƴa. Cikin gaggawa muka wuce babban asibitin gwammati dake cikin garin Adamawa, sun so mu tsaya a asibitin Girei, ni kuma nace mu tafi babban asibiti kawai, ai kuwa muna shiga na shiga cikin asibitin da hanzari dan neman agajin ma'aikatan jinya. Yaya Hamma da Amaduyal kuma suka kinkimo Dada zuwa wani dogon falo. Ma'aikatan jinyarnan da suka ga mu fulanin Daji ne sai suka banzatar da lamarinmu ga Dada ko numfashi bata yi, sai da muka yanki kati muka biya kuɗin gado kana suka sauraremu. Ward ɗin mata aka kwantar da Dada, sai dai bata samu gado ba, a katifa aka kwantar da'ita. Kasancewar ɗakin cike yake dam da marasa lafiya, rabi da kwatan majinyatan ɗakin fulanine. Wani dattijon likitane yazo kan Dada, dubanmu yayi yace. "Ku duka yaran majinyaciyarne?" Yafendona tace. "Duk yaranta ne, mu kuma ƙannenta ne" Kai ya girgiza yace. "Allah sarki, to ku ɗan dakata daga waje zan dubata, inna gama sai ku dawo ko? Amman zaku iya komawa gida ku ɗebo kayan jinya dan naga jikin mahaifiyar taku da tsanani riƙeku zamu yi. Ku tawo da bargo babba na rufa, dan zata iya jin sanyi cikin dare, wannan na asibiti bashi da kauri" Ni dai da ƙyar nake ɗaga ƙafata sabida yanda naga halin da Dada take ciki, da irin ƙanjamewar da tayi duk saina sare. Zama muka yi a bencin da aka tanada domin zama. Babu me cewa da kowa komai. Ni dai duk ɗagowar da zanyi saimun haɗa idanu da Yaya Hamma. Hankalinshi gabaki ɗaya yana kaina ko ƙibtawa bayayi. A tsaye yake yayi tsaiwa irinta fulani, irin tsaiwar da suke yi da ƙafa ɗaya, ɗayar ƙafar sai su ɗaurata akan ɗayar. Fararen kaifafan idanunshi sai yawo suke yi a jikina.." "Jabu yaushe kika dawo, ya kika baro jama'ar makka?" Cewar mahaifiyar Yaya Hamma. Shekaran jiya jirginmu ya sauka a Legos, jiya muka shiga Kano Yafendo. "Allah sarki sai kika dawo kika tarar da Adda Daso cikin jinya. Shekararta guda munata fama. Hamma shi yaita jigilar nemo mata magunguna ƙauye_ƙauye bai taɓa gajiyawa ba. Babu abinda zamu ce dashi sai dai muce Allah ya bar zumunci. Cewar Yafendona. Sai naji zuchiyata ta sake nitsewa a so da ƙaunar Yaya Hamma. Wanda zaima mahaifiyarka wannan hidimar ai dole kaji ka soshi. Murmushi nayi nace. Allah sarki. Yaya Hamma Allah ya saka maka da Alkhairi. Allah ya bar mana zumuncinmu. Boɗɗo kema ciwon kika yi ne naga duk kin fice a haiyacinki?" Na tambayeta cikin kulawa. "A'a Adda yanayin canjin rayuwane kawai, da kuma ciwon Dada,. Yaya Amaduyal wannan itace yarmu Adda Jabu" Tana faɗar haka Amaduyal ya rusuna kanshi a ƙasa yai mun sannu da zuwa, sai murnar ganina yake yi. Nima naji daɗi sosai dana sake kasancewa tare da dangina.Yaya Hamma duk wannan maganar da akeyi baiyi ko tari ba, sai ido kawai da yaketa binmu dashi. Likitan daya shiga duba Dada ne ya fito. "Mutum biyu daga cikin Yaran Daso su biyoni a baya" Yafendo sai ta nuna ni, ni da Yaya Hamma muka bishi zuwa ofishinshi, ya bamu wajen zama. "Tun yaushe baiwar Allah'nnan take cikin wannan halin kuka barta a gida saida ciwo ya cinye jikinta sannan zaku kawo mana ita? Tazo ta mutu a hsnnunmu ku ɗaura alhakin kisan a kanmu" Yaya Hamma ne yace. "Dakta ciwon zata kai shekara ɗaya da rabi haka tana yi. Amman a tsaitsaye da yin tsananinshi baifi watanni shidda ba. Sai an ɗagata sai an kwantar da'ita. Munyi magunguna gargajiya da yawa ba haka muka zauna ba" Wannan Dakta ya zare tabarau ɗinshi daga idanunshi. Ni kaina jin tsayin lokacin da Dada ta ɗauka tana jinya ya ɗagamun hankali, tausayinta ya sake ɗarsuwa a zuchiyata ai saina fashe da kuka ina salati a hankali. "Jabu kiyi shiru, kuyi haƙuri in sha Allah Dada zata tashi. Ƙarshen wahalarta a gidan Baffa yazo tunda ya rabu da'ita. Dani dake zamu iya riƙe Dada mu bata farin ciki. Dakta a faɗa mana abinda yake damunta." "To abinda yake damunta suna da yawa. Na farko shine hawan jini, dan jininta ya hau sosai, babban abinda yake damunta cutar Rawaya ce, sabida tsananta da yayi ya haifar mata da ƙurajen a hanjinta, ma'ana yaci hanjinta sosai da sosai. Dole tana buƙatar ai mata aiki ciwo kun bari yaci jikinta ainun. Akwai buƙatar ai mata ƙarin ruwa, babu ruwa babu jini sosai a jikinta. Kunyi sake da yawa, Mama na da tsawon rai ne shi yasa har Allah yasa ta kawo yanzu da ranta." Ni dai hawaye kawai nake zubarwa na tsantsar tausayin Dadana. Allah sarki baiwar Allah damo sarkin haƙuri kenan. Yaya Hamma yace. "To Dakta wanzu me ake buƙata daga ɓangarenmu?" "Akwai buƙatar kuɗi, sannan akwai buƙatar ku bata jini a ƙara mata. Da zaran mun gama duk gwaje_gwajen daya dace in sha Allah zamu sanar daku lokacin da za'ayi mata aikin. Bazai wuce jibi ba Ku dai ku tanaɗi kuɗi." Kai Yaya Hamma ya dafe da hannunshi. "To Shikenan, a bata jinina a saka mata Dakta" Dariya Dakta yayi yace. "Za'ku je lap dai a tabbatar da ingancin jinin, in yayi daidai da nata sai a ɗiba. Amman sai dai kuje ku biyu ko uku, dan leda shidda muke buƙata na jini." Tare muka fito, Yaya Hamma ya kirayi su Amaduyal suka wuce lap domin a aunasu. Ni kuma a sanyaye naima su Yafendo bayanin halin da Dada take ciki. Yafendo ina ganin ko zaku tafi gida, ni da Boɗɗo saimu dinga kwana da'ita. Asibitin akwai sanyi zai iya damunku, kuma gida Babu kowa." Kafin suce wani abun saiga Baffa Musa da Yafendo A'i hankulansu duk a tashe. "A'i am kina fama da kanki ai da kin turo Jumare yazo ke ki huta a gida. Ga dare harya rufa" Cewar Yafendo Kaɓoji. Hawaye Yafendo A'i ta share da mayafinta. "Zuchiyata ba zata samu nitsuwa ba. Yadda labarin yazo mun. Su Cubu na gidan Yaya Musa Mai Nagge ya korosu suma bayan tafiyarku. Hakan bai mishi ba ya samu Yaya Musa yake faɗa mishi wai Jabu zata gani duk abinda ya faru da'ita shine. Sannan ga yara mu mu riƙe tunda mun nuna mun fishi iko. Abun dai babu daɗi sam" Baffa Musa yace. "Ku ajjiye wannan maganar a gefe. Ke Jabu yaya jikin ita Dason?" Yafendona tace. "To jikin nata sai adda'a Yaya" Ta labarta musu abinda Dakta yace. Baffa Musa sai ya buɗe baki yana maganar su ba za'aima Dada aikiba mutuwa akeyi a asibiti, su kaza su kaza. Kuma su Yafendo suka goyu bayanshi akan hakan tare da yanke hukuncin zasu mayar da Dada gida ayi mata na Hausa. Ai saina fashe da kuka na zube ƙasa. Baffa am dan Allah kuyi mana rai Dada tana buƙatar jini da ruwa. Tana buƙatar kulawar asibiti tunda ance babu irin na hausan da ba'ayiba. Ku bari mu jarraba na asibitin" Ganina a ƙasa yasa Boɗɗo itama ta tsugunna muka ci gaba da basu haƙuri. Kundai san halin iyayen namu Fulani da taurin kai, da kuma ƙauyanci. Baffa Musa sam yaƙi yarda gashi shine mai faɗe aji a dangi kasancewarshi babba. Ni dai na koma saman kujera sai kuka nake yi Yafendo A'i tana rarrashina. A haka su Yuguda suka zo suka samemu. "Daga ina kuke Yuguda?" Buɗar bakinshi yace. "Wata likitace wai zata kwashi jinina ni na taɓa jin yadda akayi haka Baffa? Yaya Hamma yana kwance tana zuƙe mai jini wai za'a sama Dada, Amaduyal ma Yaya Hamma yace dole sai ta zuƙi nashi. Ni gaskiya bazan iyaba." Banga laifin Yuguda ba, rashin ilimi da rashin wayewa ke damunsu. "Jabu kinga duk abinda zuwa asibitinnan ya jawo ko? Mu fa a kan zuriyarmu babu wanda waɗannan mayun suka taɓa mana. Bama zuwa asibiti mu. Yuguda mu je ka kaini ɗakin shan jinin maza." Da sauri na riƙe babbar rigar Baffa. Dan Allah Baffa ka tsaya kaji. In ba'a sama Dada jininnan ba mutuwa zata yi" Sai yayi dariya yace. "Yarinya muna da maganin ƙarin jini namu na gargajiya da muke sha tun iyaye da kakanni. Daso ba za'a ƙara mata jinin maita ba." Muna cikin wannan badaƙalar wannan Dakta dake lura da Dada yazo zai wuce yaji abinda muke tattaunawa dake mutumin kirki ne kuma shima bafulataninne sai ya gaiyacemu ofishinshi. "Baffa Musa kamar yadda naji yara na kiranka ko, nasan ba lalle ka ganeni ba. Ubale ne ƙanin Ilyasu gare_gare." Da jin haka Baffa yace. "Ilyasu gare_gare abokinmu da yake ɗaya daga cikin mutanen da turawa suka ɗiba zuwa ƙasar waje dan suyi boko" Dakta yayi dariya. "Shifa Baffa Musa. To ni ƙaramin ƙaninsune wannan wanda kuke kora in zaku dandali. Wannan wanda bayan kaci shaɗin aure yake rakaka zance" Ajjiyar zuchiya na sauke jin abinda Dakta yake ce da Baffa Musa. Nasan ko babu komai zai iya shawo hankalinshi ya bar Dada a asibiti a nema mata lafiya. "Hahaha Ubale baka da mantuwa gaskiya. Yanzu shi Ilyasu gare_gare yana inane?" "Yana ingila da iyalanshi acan yake aiki shekara ashirin da biyar kenan." Baffa yace. "Allah sarki. Kai ka tura yara wai aje a tsotse jininsu Ubale? Marar lafiyar fa Daso ce ƙanwata kafa santa. Kaga ga A'i, ga Kaɓoji, ga Jabu. Waɗannan biyun yaran Dason ne, wannan kuma yaron kaɓojine." Nan Dakta ya dinga yima Baffa Musa bayani cikin hikima da dabaru irinna masu gogewa. Da ƙyar da suɗin goshi Baffa Musa ya amince yace a bar Dada a asibitin. Ajjiyar zuchiya na sauke mai ƙarfi. "To Alhamdulillah Baffa Musa, in sha Allah ba za kuyi dana sanin zuwa asibiti da'ita ba. Amman ku zaku koma gida mutum biyu sai su zauna da'ita a cikin ɗakin. So samu da namiji ɗaya ko za'a buƙaci wani abun." Baffa yace. "To Shikenan Jabu da Boɗɗo tunda sune masu jini a jika sai su zauna. Hamma ya zauna dasu ɗan baɗo dan na lura kamar ƴar gida za'ayi da Jabu" Sauke kaina nayi da sauri ina ɗan murmushi. Da haka muka fito a ƙofar ward ɗin su Dada muka ga su Hamma suna zaune a benci. Tare duk muka ɗunguma ciki, Dada na kwance ana mata ƙarin ruwa. Fuskarta tayi fayau. A gurguje suka dubata su kai mana sallama. Yafendo a tawo mana da bargo da taburma gobe in za'a kawo mana abincin safe. Akwatin kayana yana wajen Hari ki karɓa. Dafa kafaɗata tayi tace. "Allah yayi muku albarka, Allah ya baku ladan jinya. Gobe Daso zata tawo muku dashi, ita zata yo abinci daga gidanta ta kawo muku. Boɗɗo ki kunto goyon yarinyarnan asibitinnan da akwai sanyi kuji da kanku. Ita yarinyar tasha nonon shanu tunda akwai masu shayarwa." Boɗɗo ta sunto ƴarta Baban ƴar ya amshe abinshi. Yaya Hamma yace. "Jabu ku kula da Dada bari in kaisu Baffa tasha. Daga nan zan tawo muku da abinci" A dawo lafiya mu ka yi mishi. A lokacin ƙarfe kusan takwas na dare. Banyi la'asarba ga magriba da isha, ni sai yanzu na tuna. Boɗɗo bari inje in nemi wajan alwala, ke ki zauna inna dawo sai kije kema kiyi." Fita nayi da tambaya da kwatance na je wajen yin alwala da kama ruwa. A wata katuwar rumfa na hango mata suna sallah nima na shige cikinsu na rama sallolin da ake bina. Na jima sosai ina kai kukana ga Allah, tare da neman tsari a wajen Allah game da furucin Baffa a kaina na dukkan abinda ya sameni shine. Gaisawa nayi da matan dake cikin rumfar. Wata bafulatana tace. "Ai ɗakinmu ɗaya gadonmu na kusa da naku. Marar lafiyar mahaifiyarku ce?" Na dubi matar a girme kamar ba zata girme mun ba. Nace da'ita. Allah sarki, mahaifiyarmu ce" "Allah ya bata lafiya. Nima mahaifiyata nake jinya mun kai tsawon wata uku a asibitinnan muna jinyarta. Kinsan yanayin jikin tsufa, ya haɗu da ciwo" Kai na gyaɗa nace. Hakane kam. Allah ya basu lafiya baki ɗaya. "Ni sunana Sumayya, muna zaune a Girei kefa?" Sunana Jabu. Mu a ƙauyen Jere Banyo muke" Tare muka koma ɗakin jinya da Sumayya, muna tafe tana jana da hira har muka iso inda Dada take kwance. Da Boɗɗo suka gaisa. Nina na ƙarasa naima mahaifiyarta Yaya jiki, tana zaune tana shan kunu. Komawa nayi kusa da Baɗɗo. Dada bata motsa ba Baɗɗo tunda na tafi?" Shiru Baɗɗo bata ma san inayi ba hankalinta baya asibitinnan da halama yayi nisa. Na lura bayan ciwon Dada akwai matsalar dake nuƙurƙusan Baɗɗo shine ma dalilin ramarta. Kafaɗarta na dafa sai tayi sauri ta kalleni. Komai yayi tsanani maganin yana ga Allah. Baɗɗo je kiyi Sallah ki dawo ki sanar dani damuwarki, zan taimaka miki ko da da adda'a ne." Bata ce komai ba ta fita. Ni kuma na ƙurama Dada idanu sai numfashi taie ja tana saukewa, ga wani irin sanyi da akeyi, damma ɗakin da jama'a sosai gadajen marasa lafiya zasu iya kaiwa guda talatin. "Jabu ga abinci kuci naga kamar ba'a kawo muku abincin ba tukunna ko?" Na jiyo muryar sumayya a bayana da kwanon samirah a hannunta. Nasa hannu na amsa. Mun gode Sumayya. E ba'a kawo mana abincin ba tukunna dai, nafa gode. Murmushi tayi mun tace. 'ai mun zama ɗaya Jabu, ki saki jiki duk abinda kike buƙata ki tambayeni kawai." To Shikenan Sumayya." Kwanon abincin na ajjiye a gefen katifar da Dada take kwance. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI. 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 18 Dana sunkuya sai naji sanyi sosai yana busowa ta ƙasan gadajen marasa lafiya. Nayi maza na cire hijabina na sake lulluɓema Dada kanta dashi, na gyara mata kwanciyarta, ko fulo babu a gadon. Dama jar abayace a jikina mayafinta yana ɗaure a kaina saina cire mayafin nayi yafe irinna takari mazauna saudiyya. Nayi zamana a gefen katifar Dada. Likitocine suka shigo ward ɗin, suna bi gado_gado suna duba marasa lafiya tafe_tafe har suka iso namu wajen. Fayal din Dada suka buɗe suka ɗan duba. Suka auna bugun zuchiyarta, da zafin jiki, sai wata allura da suka ƙara mata a cikin ruwan dake ɗaure a hannunta. Ruwan sai yafi minti biyar yake ɗigowa. "Sannu ko Allah ya bata lafiya. Gobe za'ayi sallama sosai a ɗakin zaku samu gado da safe. Amman ya kamata ku nemo bargo wanda zaku yi amfani dashi sabida akwai sanyi sosai. Sannan ƙarfe biyu ruwan dake ɗaure a hannunta zai ƙare, to zaki iya nemana a office ko?" Godiya nayi ma Daktan suka wuce zuwa gadonsu Sumayya. Sai ga Baɗɗo ta dawo. Baɗɗo zo ga abinci kici naga kamar jego kikeyo ko naga goyonki ƙaramine" Ta zauna ta soma cin abincin kenan muka hango Yaya Hamma da kaya niƙi _niƙi, bargone, tabarmane, da bakko ɗauke da filas na ruwan zafi dana abinci. Da sauri na tareshi a hanya na amshi bargon. Murmushi mai taushi ya sakarmun yana ƙaremun kallo. Nima murmushin na sakar mishi har saida haƙoran makkana suka fito. Sannu da dawowa Yaya Hamma" "Sannu Jabuna" Ƙarasawa mu ka yi. Yaya Hamma da kanshi ya shinfiɗa mana tabarma a gefen katifar Dada. Bargon daya kawo saina rufa ma Dada na cire na asibitin nass a gefe dan wanda ya kawo da gani yafi ɗumi. Abinci ya ciro a cikin bakkonnan. Filas ɗin ruwan kuma ya miƙo mun na ajjiye a gefe. Harda gwangwanin madarar gari kwalin lipton, sai sigar kwali mai zaki, wasu na kiranta mai iyali. Da ruwan Swan na gora manya biyu sai kofuna, da robobin cin abinci, da lokali. Allah ya saka da Alkhairi sannu da ƙoƙari a darennan ka koma gida Yaya Hamma?" "Ai dole in koma, tunda kinga mun fito hankali ba a kwance ba ba'a ɗakko komai ba. Dole ana buƙatar bargo tabarma, abinci shima dole aci. Baɗɗo zuba muku abincin kuci. Ni zanje wajen maza a waje in zauna. Jabu in kinci abinci ki sameni a waje" To Shikenan Yaya Hamma mun gode ƙwarai" Baɗɗo ta zuba mana jallof ɗin taliya da wake taji bushasshen kifi. "Aradun Allah ba Hama bace tayi wannan abincin ba. Ai mu tuwo muke ci kullum. Ko ita tayi ai ba zata bari Hamma ya kawo miki ba." Bayan na kai nomar taliyarnan bakina sai nace. Me yasa kikace haka Baɗɗo?" "Adda Jabu Hama macece mai mugun kishi kasancewarta fulanin Camaron. Daga can suka yi ƙaura suka dawo Banyo. Tunda labarin soyayyarki ke da Yaya Hamma ya faso cikin Jaɓɓi hatta ni Hama zaman gugar jigida muke yi. Adda Daso kuma bayan tafiyarki ta dinga kunno da maganganu iri_iri, suka ɗinke da Hama. Har wajen Malami suka je, wai a ɗauke hankalin Yaya Hamma daga gareki. Dan ya shiga kewa da damuwar rashinki sosai. Wannan ramewar da kika ga yayi duk na tunaninki ne. Saboda ke ya sai salula burinshi kawai yaji labarinki. Ya sake ninka hidimar da yake yima Dada duk sabida ke." Baki na riƙe ina mai cike da mamakin Daso. Da mamakin irin son da Yaya Hamma yake yi mini, son da kunya da ƙauyanci suka hana a furta mun. Amman ina kyautata zaton a darennan zai sanar dani tunda dai nadawo. Ke Baɗɗo kinsan abinda kike faɗe kuwa. Dason da ita za'a haɗa baki dan a cire ma Yaya Hamma sona tana jinina, kikace sun ɗinke da Hama?" "Nasan abinda nake faɗa Adda. Adda Daso bata sati sai tazo wajen Hama, haka itama Hama bata kwana biyu sai taje gidan Adda Dason. Su shiga ɗaki suita ƙus_ƙus" Kai na jinjina nace. Dason tayi aure kenan?" "Ta yi aure a Girei har da ƴarta mace Meramu" Ajjiyar zuchiya na sauke. Da naji a inda tayi auren. To amman ke yaya akayi kikasan sunje wajen malami dan a ɗauke hankalin Yaya Hamma a kaina?" "Adda wallahi sunje. A bakin ƙawar Adda Daso naji wannan labarin. Wajen zamanmu ɗaya inda muke kai nono. Ni ina siyar da nono zalla, ita kuma tana siyar da dambu, da fura" Hmmm to ta Allah ba tasu ba. In Allah ya ƙaddari zamu yi zaman aure ni da Yaya Hamma, Babu wani mahalukin daya isa ya shiga tsakaninmu. Haka in Allah bai nufa ba, duk yadda muka kai ga son hakan to bazai yiwu ba." "Hakane Adda Jabu. Yaya Hamma gaskiya yana sonki sosai. Kuma yana da sauƙin kai duk da Hama tana tunzurashi wasu lokutan " Haka dai muka gama cin abincinmu, tana bani labari. Bari inje in sami Yaya Hamma ina zuwa. Ki dinga lura da Dada." Miƙewa nayi na fice daga ɗakin. A takure a wani benci na hango Yaya Hamma yana saye da wata koriyar suwaita ya tuttura hannayenshi duka biyu a ajjihun rigar. Yana hangoni ya miƙe. Muƙu_muƙun sanyi akeyi musamman a wajennan, cikin dake akwai numfarfashi da yawa sanyin bai kai na wajen ba. Isowa nayi inda yake da sallama a bakina. "Ameen wa'alaikis salam babbar mace, ina mai farin cikin sake yin tozali dake a lokacin da banyi zato ba balle tsammani. Dan mafarkaina a kanki nuna mun suke yi kamar kin barni har abadane ɗauke da nauyin da babu wata mace da zata iya sauke mun face ke. Barka da shigowa najeriya" idanu muka ƙurama juna. Wallahi soyayya duniya ne, jina nake tamkar akan yaya Hamma na soma soyayya a kab rayuwa. Son da nake yi mishi a yanzu ya doke son da nayi ma Burodami Debisi. Kazalika ya doke son da nayi ma Gwadabe. Illahirin jikina amsa saƙon soyayyar Yaya Hamma yake yi wanda yake isarmun ta cikin fararen idanunshi. ( Iyabo yau bake ba bacci dan su Khadija maidoki , m Farida Ammar, ummu nabeeha, maman yasser, maman Twins, Uwal matasa da sauransu sun isheki. Mamanmu Hajara Aliyu dai bansan ko zata yi muku uziri ba) A tarihi ansan Fulani da jarumta wajen nuna soyayyarsu ga mace, hakanne yasa kafin saurayi ya samu matar aure dole saiya fito filin shaɗi ya nuna jarumtarshi kafin ya samu abokiyar rayuwa. Matansu kuma sunfi son jarumi ba lusari ba, jarumin da zai fito filin daga ya nuna bajintarshi. "A ina alƙawarin da kikai mun ya kwana. Ina fatan babu wanda kika mallakama zuchiyarki?" Idanu na lumshe bansan sanda nace dashi. Babu wanda na bashi damar samun gurbi a zuchiyata Yaya Hamma. Na kasance mai girmamaka fiye da tunaninka." Wajen zama ya nuna mun da hannunshi. Dariya nayi mishi na zauna, shima ya zauna muna fuskantar juna. "Bani labarin tafiya, da fatan kunci nasarar samun abinda aka fita nema ko?" Alhamdulillah abinda akaje nema an samo. Da ba dan na shigo na tarar da Dada babu yadda take ba, dama da maganar siyan gida zan yi. In ɗauketa daga cikin wahalar da take ciki. To Allah Allah ya yanke mata wahalarta, sai dai muyi fatan Allah ya bata lafiya " "Ameen. Ba dai sayen gida ba, sai dai sayen fili ko? Yuguda yana harkar gini koshi zai gina mata ɗan ɗakin da zata yi rayuwarta, da ɗakin du Cubu. Yusufu shi yana can gidan yana kiwo shi Baffa bazai bari ya dawo hannun Dada ba." Dubanshi nayi nace. Filin yana iya kaiwa nawa Yaya Hamma? Dan da so samune so nake kafin a sallami Dada an gama komai sai ta tare a gidanta in Allah ya tashi kafaɗarta, dan nasan ba zata amince ta bar mahaifarta ba". Dariya yayi mun yace. " Tab ai mutuwace kaɗai zata iya raba Dada da Jaɓɓi lamba In akwai kuɗi a hannunki filaye akwaisu, me gari zan samu ya nuna mun filayen dake ƙasa sai mu siya yasa hannu a baki takaddarki, filin baya wahala har masu saye ake nema. Ko filin dubu talatin ya isa a fitar da ɗakuna uku da tsakar gida da banɗaki" Abinka da ƙauye ni kuma a lokacin akwai kuɗi a jikina sai nace. To a nema mun guda biyu a waje daban daban Yaya Hamma zan siya" Kallona yayi yace. "Me zaki yi da biyun?" Nima shi nake kallo nace. Inaso zan ginane in ajjiye a matsayin kadara kudun kar kuɗin su lalace" Sai yayi murmushi ya fuskanceni da kyau yace. "In kina jin maganata A'a ba zaki siya ba. In kadara kike so ki sai shanu ko awaki ki ba Amaduyal ko Yusufu su dinga kaɗasu jeji suna miki kiwonsu. Yanzu zaki zama Hajiya. Fili ko gida a ƙauye irin namu bashi da wata daraja. Abin kiwonki kuwa kullum daraja suke sake yi, kuma ko da yaushe kika matsu zaki siyar da abunki ki karɓi kuɗinki ba tare da wani ma yasan halin da kike ciki ba" Jinjina kai nayi, na kuma yi na,am da wannan shawarar. Shirune ya biyo baya na wasu lokuta. Ko wanne cikinmu da abinda yake juya tunaninshi. "Jabu" Naji ya ambaci sunana da wata iriyar muryar data tayar da tsigar jikina, wata kasalace ta sakko mun da ƙyar na samu zarafin amsawa a hankali. "Yanzu in ɗan ƙauye kamata yace zai aure ki kina ƴar birni kuma Hajiya zaki bashi dama ya aureki?" Wayyo Allah daɗi inji ɓarawon takanɗa a raina nace anzo wajen. A fili kuma nace. Me zai hana in aureshi matsawar yayi mun? Zaman birni, da zuwa Saudiyya ba hujja bace da zan riƙe wacce zata nesantani da abinda nake so ba." Shiru yayi yana nazari can sai ya furta. "Ina sonki Jabu. Tun lokacin da labarin mutuwar aurenki yazo kunnena naji kin kwanta mun a raina. Tsoro da fargaba su suka hanani fasa wannan sirrin. Amman abun mamaki labarin sonki da nake yi ya karaɗe Jaɓɓi. Jabu zaki iya aurena kiyi rayuwa dani kamar yadda matanmu suke rayuwa damu, zaki girmamani ki yi mun biyayya kamar yadda matanmu ke yi?" I danuna na lumshe sanyi da nitsuwa suka ratsa zuchiyata da dukkan rassan jikina. Allah kawai nake ambato a zuchiyata. Yaya Hamma tabbas nima ina sonka, mu ba ƙananan yara bane munsan menene so, haka munsan ƙiyayyar itama. Amman me yasa baka sanar dani kana sona ba a lokacin da zan tafi Saudiyya ba?" Dariya yayi, ya damƙe hannunshi halamar yana cikin farin ciki. "Wauta, da tsoron kar in faɗa miki zumuncin da muke yi ya lalace, ni baki soni ba, kuma zumunci dani ma ki ƙiyi. Amman ko a filin jirgi naso sanar dake kwarjini ki Kai mun. Amman na sanarma da Dada ƙudurina kuma tasama abun albarka tayi farin ciki, babu mamaki ƙila sunyi maganar da Dadarmu amman bata ce mun komaiba kasancewar akwai kunya mai tsanani a tsakaninmu" To naji. Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi. Amman wani hanzari ba gudu ba. Bazan ɓoye maka ba, zanyi maka dukkannin irin biyayyar da ba kai zato ba. Amman bazan iya ɗaukar tallar nono ba gaskiyar magana. Amman inaso zan dinga kasuwancin kaya tsakankanin ƙauyannan, zuwa cikin gari, dan nayi sarin kayayyaki iri_iri. Amman batun tallar Nono babu shi, ka amince ko kana da ja?" Duk wannan maganar kaina a ƙasa nake yi mai. Ya jima bai bani amsaba yana nazari can sai naji ya nisa yace. "To Shikenan. Indai tallar nonone bakya so, to ba zaki ɗauki tallar nono ba Jabu. Zanyi iyakacin ƙoƙarina na ganin na fahimtar da duk wanda zai kawo tsokaci. Babu damuwa in Allah ya yarda, fatanmu Allah yaba Dada lafiya yasa albarka a cikin lamarin. Yau abinda ya tsaya mun cak zai barni in huta." Dariya nayi cikin zolaya nace. Menene ya tsaya maka?" Ya bani amsa da cewa. "Baki ga na rame ba? Ai tunaninki ne kawai yaketa ɗawainiya dani. Ko wajen aiki naje tunaninki baya barina inyi sukuni. Musamman in ina cikin daji da shanu, nafi ware lokaci na musamman ina hango irin rayuwar farin ciki da soyayyar da zamu gudanar a cikin ɗakinmu. Jabu zansa ki mance duk rayuwarki ta baya nayi miki alƙawari.' Mun daɗe sosai muna musayar kalaman ƙaunaa dan nima ba'a barni a baya ba. Zagewa nayi na dinga zaro mishi zaren maganganun ƙauna mai sanya nutsuwa da annashuwa. Daga ƙarshe ya rakoni har ƙofar ɗakin majinyata muka rabu kamar ba zamu rabu ba tsabaragen shauƙin juna. Na tarar da Baɗɗo tayi baccinta ta duƙunƙune da bargo. Dada ma sai baccinta take yi. Majinyatan ɗakin kusan rabinsu duk sunyi bacci. Dada na zuba ma idanu ina mata sdda'ar Allah ya tashi kafaɗarta taga aurena da Hamma. Ina roƙon Allah ya bata tsawon ran da zata goya ɗana da zan haifama Yaya Hamma a bayanta. A wannan daren in banda shauƙi babu abinda ke ɗibana. Tunanina yayi zurfi ya kaini har zuwa tsufana a gidan Yaya Hamma yaranmu suma sun girma, wai gamunan har a tsufan Yaya Hamma bai dena alfahari dani ba. "Baiwar Allah " Naji wata mata ta ambaci sunana ashe ma'aikaciyar jinyace har ƙarfe biyu tayi tazo sake ma Dada ruwan dake ɗaure a hannunta. Matsa mata nayi tayi aikinta, Dada dai bata farka ba, nima a haka bacci ya kwasheni zuwa asuba duk akayi waje damu, za'ayi shara a yi mopping kana a sake ma marasa lafiya zanin gado. A wannan rumfar muka haɗu da Sumayya bayan munyi Sallah muka gaggaisa ssi take cemun. "Bari inje in ɗaura girki kafin masu shara su gama gyaran ɗakin jinya. Girki kuma Sumayya, anan kuke girki?" Sai tayi dariya tace. "Anan nake yi. Gudun ɗaurama mutane wahala kinsan nace miki mun jima sosai a asibitin shiyasa. Bazai yiwu ace kullum sai an kawo muku abinci ba" Ksi na gyaɗa maganarta gaskiya ne. Bakin ƙofar ɗakin jinyar muks koma, muns zama Yaya Hamma yana ƙarasowa. Ina kwana Yaya Hamma?" Na faɗa a ladabce fiye ma da na da. Shima ya amsani a mutunce fiye da jiya. Suka gaisa da Baɗɗo. "Yaya jikin Dadan, ta farka kuwa?" Baɗɗo ce ta bashi amsa" "A's bata farka ba tukunna dai. Amman sunce zata farka yau" Shirune ya biyo baya kowanne da abinda yake lissafawa a zuchiyarshi. Ƙarfe takwas daidai aka bads izinin masu kula da masu jinya zasu iya komawa. Tare muka shiga ciki mu uku. Dakta muka gani a tsaye a kan Dada yana dubata, wani irin amai take yi kamar zata amayar da duka hanjinta, harda jini_jini a cikin aman. Ba shiri wannan Dakta ya kira wasu ma'aikatan kiwon lafiya mata suka kawo gadon tura marasa lafiya aka ɗaura Dads. "Zamu shiga da'ita ɗakin tiyata da gaggawa, ku biyoni maza" A gaggauce Dakta yayi maganarshi gabaki ɗaya hankalinmu ya tashi ganin halin da Dada take ciki. A bakin ɗakin tiyata muka tsaya, Dakta yaima wata mace magana, shi ya shige da Dada ita kuma tace ni in biyota. Binta nayi ta bani takaddar sanya hannu da kuɗin aikin a rubuce. Ta nuna mun windon da zan kai takaddar in biya, inna biya in dawo mata dashi. Nafi awa biyu anata cuku_cuku na biya duk abinda ake buƙata na dawo na tarar da su Yaya Hamma a bakin ɗakin tiyatar sunyi jigum. Ga wasu iyalanma munzo mun tarar dasu jigum_jigum da halama wani nasu suma suke jira a fito dashi. Kamar awa guda da zamanmu aka buɗe kofar ɗakin tiyatar aka tuƙo wata dattijuwar mace. Wannan iyalan suka bi bayan gadon suna hamdala. Da idanu na bisu ina fatan muma a fito da Dada lafiya cikin nasara. "Jabu bari in fita daga harabar asibitin kar su Baffa suzo su tarar Dada bata ɗakin jinya. Zan dinga leƙowa." Kai kawai na iya gyaɗawas, ya wuce nabi bayanshi da idanu har saida ya ɓace. Hawayen daya gangaro a kumatuna nayi saurin sharewa. Awa ɗaya awa biyu muna dai zaune. Yaya Hamma na leƙowa yana dubamu. Su Baffa Musa ma sun iso, da su Daso harda Hama. Amman su suna can wajen ɗakin jinya suna jira. Baffa Musa ne kawai yazo ya dubamu. Ni a lokacin babu abinda nake yi sai kuka kawai. Awan Dada uku a ɗakin tiyata Allah cikin ikonshi aka fito da'ita a gadon marasa lafiya. Muna biye da gadon ni da Baɗɗo mum riƙe hannun junanmu gam. Su Daso suna zaune a tabarma muka wuce ciki. Anyi sallama a ɗakin sosai muma mun samu an mayar da Dada gado. "Mun mata aiki cikin nasara yanzu jini zamu ƙara mata. Sai zuwa gobe zata samu farkawa. Tana farkawa kuyi maza ku kira Dakta, kar a bata komai taci. Allah ya ƙara sauƙi" Ameen mungode Dakta" Na amsashi. Ina zaune a kujera na tusa Dada a gaba sai hawaye nake zubarwa, zuchiyata tana ɗaci. A cikin wannan yanayin su Baffa Musa suka shigo suka riskeni Baɗɗo sai baki take bani. Daso ta matso kusa daf dani ta riƙe mun kafaɗa, mutum baida kama. "Kiyi haƙuri Jabu. Ayi ma Dada adda'a Allah yasa anyi tiyatar a sa'a, Allah ya tashi kafaɗunta." Ameen Daso mungode, sannunku da ƙoƙari" Baffa ma yace. "Ayi haƙuri, ciwon uwa akwai ɗaga hankali. Kuma duk mai rai mamacine, in Daso shan ruwanta bai ƙare ba ko ciwon da take ciki yafi wannan zata tashi. In kwananta kuma ya ƙare tana gaɗa tsabar lafiya saita faɗi ta mutu, ayi haƙuri" Kai na gyaɗa ma Baffa kawai. Hama cikin dakewa kamar ba itace wannan mai fara,arba tace. "Sannu Jabu. Baɗɗo Allah ya ba Dada lafiya" Ameen hama mungode sosai. Haihuwa kikayine?" Dan na ganta da sabon goyo ɗanye sharab. Baɗɗo ce tace. "Haihuwa tayi gobe za'ayi suna. An samu mace" Allah sarki Allah ya raya mana su." Na faɗa a sanyaye. Yaya Hamma yace. "Ki bata jaririyar ta ganta mana Hama" Da fullanci yayi Maganar, saida ta mayar mishi da amsa kafin ta sakko yarinyar ta miƙa ma Daso, ita kuma Daso ta miƙo mun. Bismillah nayi na amshi yarinyar a tsumman goyo, yarinyar na ƙarnin nono. Zanin goyon na warin hammata . Dan hammatar Hama cike maƙil take da gashi har wani ja yayi da wani dattin fari.Yarinyar fara sol, ga gashi duk ya lulluɓe goshinta da gefen kunnenta. Yarinyar takai minti biyar a hannuna na miƙa ma Daso ita. Allah ya raya mana" Daso ce ta amsa, Hama kuwa bakinta ko motsawa baiyi ba. "Jabu ga abinci mun kawo muku. Da yamma matar Amaduyal zata kawo na dare. Dadanmu tace zata zo da rana inta gama tallan Nono " Da hanzari Baɗɗo ta buɗe ledar abincin. Tuwon masarane da miyar kuka da nama a ciki. Ta zuba nata ta zauna ta soma ci. Ni kuma na haɗe musu kan kwanukan jiya nasa musu a leda. "To mu kam zamu tafi. Ni na bari ana dafa mun Nono" Cewar Daso. Godiya muka yi musu. Baffa Musa yace shima kiwo zai tafi dan haka zai koma. Ya zaro dubu biyar ya bani yace in riƙe a hannuna. "Nima zanje in dawo Jabu. Ba jimawa zanyi ba" Cewar Yaya Hamma. Ledar kwanukan abincin jiya na miƙa mishi. Mu kai musu sallama suka fita. Ajjiyar zuchiya na sauke na zuba tuwonnan da nama yanka biyu. Babu maggi acikin miyar sai gishiri haka na tuttura na kora da ruwa yinwa nake ji sosai. Tea na haɗa kofi ɗaya na kwantar da wannan tuwo. Yaya Hamma baifi Awa uku ba ya dawo, ya dawo ya tarar an ɗaurama Dada ƙarin jini. Mu kuma har munje munyi sallar azahar mun dawo muna zaune muna ɗan hira ya shigo. Sannu da zuwa mu ka yi mishi. Wanka yayo dan har kaya ya sake da suwaita da hular sanyi duk ya canja. "Jabu anfa samu gidan siyarwa. Abokinane zaiyi aure shine yayi gini. To auren yasha ruwa sakamakon wuta da uwargidanshi ta buɗe. To shi yace da zai samu mai siyan gidan shi ko nawane daya siyar. Gidan babbane ɗakuna biyarne, sai madafi da banɗaki. To me kika gani?" To Yaya Hamma in kana ganin babu wata matsala ai ni dama nafison in siya gida ba fili ba. Nawa kuɗin gidan?" "To da na nuna mishi ke zaki siya, yace mu kawo dubu sittin da bakwai. Amman yayi sauƙi sosai ni dai nace sittin zamu biya. In yayi miki ki ƙirgo kuɗo yanzu sai in koma in bashi, gobe zaki ganshi ya ƙaro shanu." Jakata na zuge na ƙirgi kuɗinnan cas na ba Yaya Hamma. "To saina dawo bazan jima ba" Yasa kai ya fice murmushi nayi na cikar burina, hatta wahalar da nasha domin tara kuɗin da zan sa Dada murmushi ya zama tarihi. Wajajen ƙarfe biyar na yamma saiga Amaduyal da matarshi, da Jatau da Hari. Sun tawo dubiya. "Amaduyal sai yanzu?" Na tambayeshi, shida ya dace sassafe ace ya tawo. Matar tashi ma sai yanzune taga damar zuwa, surukarta bata da lafiya" "Baffane ya riƙeni Adda, kuma tun duku_duku yasani a gaba muka tafi kiwo. Kari kuma sai nace tayi abinci ta jirani muna dawowa sai mu tawo. Kiyi haƙuri Adda amman wallahi jiya ga Kari ko rintsawa banyiba. Tunanin halin da Dada take ciki ya dabaibayeni" Ajjiyar zuchiya na sauke kana nace. To Shikenan Allah ya kyauta. Kaje ka dubo du Cubu kuwa, a wanne hali suke?" "Naje, suna cikin damuwa sosai. Baffa dsi yana ƙarfafasu, a bakinsu naji labarin anyi ma Dada tiyata" Hari ta katse mana zancanmu ta hanyar gaisuwa. Jatau yace. "Amaryarmu Yaya jikin Dada?' Ɗan dariya nayi mishi kawai. Hari sai zolaya take faman yi. "Jabu wannan matar Amaduyalce sunanta Kari. Kari wannan itace yar Amaduyal" Matsowa Kari tayi ta tsugunna muka gaisa tare da tambayar me jiki. Jiki da sauƙi Kari muna jiran farkawarta tukunna." Sai ɗa su Kari su kai magriba sannan suka ɗau haramar tafiya gida. Nera dubu goma Amaduyal ya zaro ya bani. Jatau kuma ya bani nera dubu biyar. Sallama dasu suka tafi. A hanyata ta dawowa daga sallar isha na hango Yaya Hamma daga nesa yana tafe kici_kici da manyan ledoji a hannayenshi. A gaskiya Yaya Hamma mai ƙoƙarine sosai. Tunda muka zo asibitinnan yake ta faman hidima damu, da ajjihunshi, da jikinshi, da lokacinshi baki ɗaya. Bayan munyi sati guda a asibiti Jikin Dada ya soma yin sauƙi duk da har zuwa wannan lokacin bat gane suwaye a kanta. Yaya Hamma ya koma bakin aikinshi a asibiti yake kwana ko za'a buƙaci wani abun, da sassafe saiya shirya ya wuce wajen aikinshi dama a cikin birni yake aikin. Ni da Baɗɗo nakanje gida, in huta in yo mana girki sai in dawo, itama takanje ta wuni a gida ta dawo. Miyar stew nayi mana mai yawa sai muke siyan farar shinkafa dafaffiya a bakin asibiti, ko kuma mu sai biredi mu dangwala da miya tunda bama rabo da ruwan zafi, dan abincin da ake kawowa gashi ga kamarshi miya ce kamar an wanke kan mahaukaciya. Anan zan dakata sai mu tara gobe in Allah ya nuna mana. Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 *Ƴar uwa ina fatan baki mance da kayan ƙamshin Mrs Bukhari gidan ƙamshi ba ko? Ƴar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ƙamshi. Matso kusa ƴar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ƙamshi ya riƙe miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake saƙawa a tsakankanin kaya. Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ƙamshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata. Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haɗe da turaren fesawa a gashi. Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ƙara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ƙamshin kifi ɗanye. Inada humrori kala_kala. Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ƙamshi. Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ƙamshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ƴar mutan Maiduguri kin samu ƙamshi. ( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai ɗauke da abubuwa huɗu manya kuma a kan kuɗi ƙalilan karki bari garaɓasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)* Ku Shashe takaicinku da wannan page ɗi. Ƴan bati an gaisheku inata sauraren comments daga gareku kuma ba'a barku a baya ba. NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 19 Maraɗi Gwadabe Yana fitowa daga ɗakin Hadiza ya sauke ajjiyar zuchiya sassanya. Tsaki yaji an doka daga gabanshi, ɗagowar da zaiyi yaga ashe Baba Asshi ce a tsaye da yaranta da matansu a tsakar gidan suna ƙus_ƙus. "Ina wuni Baba Asshi?" In kun tanka Baba Asshi ta tanka. Saida ya wuce ta sake jan wani dogon tsakin, kanshi kawai ya gyaɗa yana fata da burin kar a samu irin wannan rarrabuwar kan a nashi gidan. Da sallama ya shiga ɗakin Amarya Shafa. Tana zaune akan kujera tasha adon atamfarta baƙar macce ƴar leda. Bakinnan nata yasha janbaki raɗau sai sheƙi yakeyi. Komai zaune yake daram a muhallinshi. Da sauri Shafa ta miƙe ta tawo da sassarfa izuwa wajen mijinta. Isowarta ke da wuya ya haɗe jikinshi da nata ya riƙeta gam. Ajjiyar zuchiya ya sauke mai ƙarfi a zuchiyarshi yace.."Lallai aure ni'imace akwai hikima a auren mata biyu, shi yasa ubangijinmu ya umarcemu da somawa da biyu madamar zamuyi adalci. Ko wacce mace da irin ƙamshinta, taushin fatarta, kalaminta, Sannan da irin baiwar da Allah subuhanahu wata ala yai mata. A wannan daren Amarci Gwadabe ya gwangwaji Amarcinshi lami lafiya kuma Alhamdulillah Shafa ta kawo cikakken budurci marar kokonto a cikinshi. Tana kwance a ƙirjin mijinta tana baccin daɗi da wahala zuchiyoyinsu fes. Ta ɓangaren Hadiza kuwa tana kwance tana lissafe lissafe gami da hasaso abinda bazai taɓa bata kwanciyar hankali da nutsuwa ba. Dan a wannan daren sai da ta dinga tambayar kanta to waima me yasa ta amince da Auren Gwadabe ne ma?" Nasihu da surruka, da dabarun zama da kishiya, da zama tauraruwa a idanun miji da Baba Fhatsima ta karanto mata, shi ya sake faɗi mata. Wasu zafafan hawaye suka gangaro suka wanke mata kumatunta. Zurub ta miƙe ta faɗa banɗaki ta ɗauro alwala ta koma ɗakinta. Ta maye gurbin tunane_tunanen da basu da amfani da yin sallolin nafila tana miƙa kukanta ga Ubangiji kan ya sassauta mata kishin dake zuchiyarta. Yaa kuma kareta da cutar da abokiyar zamanta koda da furucine. Ya ɗaga daraja da kimarta a idanun mijinta. Haka ta dinga sallah tana adda'a, ai kuwa saida taga bacci yana shirin kayar da'ita sannan ta kwanta. Ta kuwa samu bacci mai nutsuwa kuma nannauya. Asubar fari ta miƙe ta nufi kitchen. Dai_dai Shafa itama ta buɗe ƙofar ɗakinta ta fito kitchen. Idanu suka haɗa duk da dai akwai duhu amman sunsan juna suke kallo. "Yaya barka da asuba" Shafa ta faɗa tana ƙoƙarin buɗe kitchen ɗinta. "Yauwa barka dai Amarya mai maganar suger. Ya kwanan angon naki?" Shafa tayi murmushi ta ɗan sauke kanta ƙasa bata ce komai ba dai. Kitchen Hadiza ta faɗa tana murmushi, amman a baɗini zuchiyarta ma bugawa yake yi, hatta hannayenta sai taji suna rawa kakakar_kakakar. Cikin zuchiyarta tace. "Kishi bala'ine. Gaskiya mana a gidanmu aka kasa samun dedeto. Ashe haka kishi yake da tasiri mai girma?" Hawayen dake shirin zubowa a idanunta ta mayar da hanzari. A gurguje ta kunna risho ta faɗa banɗaki bayan ta ɗora ruwan wanka. Jikinta a mugun mace ta fito daga banɗakin, daidai Gwadabe ya fito daga ɗakin Shafa zaije wankan tsarki. Shafar tana biye dashi da dukkan halamu tare zasu je suyi wankan. Lallai soyayya ta kai soyayya. Murmushi ta sakarma Gwadabe, murmushin daya kasance tamkar garwashi wajen ƙuna. Shigewa tayi ɗaki tana haki. A daddafe tayi ra'atanil fajir, ta ɗaura da sallar asuba. Ta jima sosai akan sallaya tana roƙon Allah ya sa mata salama a zuchiyarta game da wannan kishi mai kai mata mahallaka ya baro. Saida ta karanta Qur'ani suratul naba'i ta shafa adda'a sai taji zuchiyarta tayi wasai. Cikin sauƙin zuchiya ta shalla wanka, ta shiga gyaran ɗakinta cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala, a madadin kunna turaren wuta tunda bata da gawayi kuma yayi wuri ta aika gida a ɗebo mata saita kunna ɗan tsinke ta bishi da Room freshener na MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI mai ƙamshin oud Cikin ƙanƙanin lokaci gidan ya ɗauki saiti. Zama tayi a barandar data haɗa ƙofofin uku, tana iya hango masu gilmawa, suma suna iya hangota. Doya ta gutsura ta fereye kaɗan, ta ɗaura abun suyanta ta zuba mai ta soma suyan doya. Matar Sabitu ce ta fito tsakar gidan taci uban ƙananun kaya kanta babu ko ɗankwali kasancewarta mai gashi daidaiya, sai karairaye takeyi da ledar shara a hannunta ta gangara ƙasan gidan dan jefar da ledar shara a babban durom ɗin shara dake gefen bayan gidan tsakar gidan. Kai Hadiza ta jirjiza kawai. Doyarta ta soyu ta kwashe ta juye man a samira ta adanashi. Sai ta mayar da kaskon kan wuta ta fasa ƙwai biyu ta yanka albassa ta ɗan barbaɗa dunƙule ta soye ƙwanta gidan ya kaure da ƙamshi. Da ɗaya da ɗaya amaren gidan suketa fitowa domin ɗora abinda za'a durama ƴan hanji, dama dai kunsan Amare a gigice suke tashi da yinwa. Ruwan tea Hadiza ta haɗa dama tana da ruwan zafi a flaks ɗinta. Ta gama haɗa kayan karyawanta tsab ta kai ciki. Ta yafa mayafinta da ƙaton kaskonta me murfi ta fito tsakar gidan. Ta haɗu da matar Abdullahi da matar Jazuli, babu wanda ya kalleta itace dai ta gaishesu a wani wulaƙance suka amsata har suna shewa, ko ta mecece ohon musu dai. Ɓarayin su Yaya Tasi'u ta nufa. Da matar Yaya Jamilu ta soma cin karo Innar Khadija. Tana soya dankalin turawa a ƙofar kitchen ɗinta a gawayi. Tayi kaca_kaca da wajen, ɓawon dankalinma da ɓaron ƙwai duk ta zubar a ƙasa yara sun tattaka. "Me zan gani Amarya sassafe haka. Af na mance ashe zawara kwana uku akeyi mata ango ya koma ɗakin Amarya ko?" Ɗan murmusawa Hadiza tayi, inda sabo ta riga da tasan dama irin zaman da akeyi. Magana ta arziki bata haɗa kowa da kowa, face habaici da son gumama juna. "Hakane ango yana ɗakin Amarya. Nima gaushi nazo ku bani" Sai ta tuntsure da dariya tace. "Ga gaushi zo ki ɗiba kafin ku soma hura naku. Tunda me gidan maganin ƙarfin maza yake siyarwa" Ajjiye kaskon tayi, domin furucin Innar Khadija yayi mata zafi. Sun daɗe suna kushe sana'ar Gwadabe a cikin gida. Dan Amaryar Malam har yara take turawa da nera ɗari tace wai a bata maganin basir malam zata ba. "Bari in gaisa da Anty Badi'a tukunna sai inzo in ɗiba." Nan ta wuceta ta barta da zunɗenta ta baya. Tun daga kofar da zata sadaka da ɓarayin Anti Badi'a kake jiyo ƙamshi na tashi. Falonta tsab yasha gyara, ta shiga ta samu Sailuba na fesa Room freshener a labulayen ɗakin. Anty Badi'a data ci kwalliya da riga da sikert ɗan kanti wani mai tattara na zamanin tana gaban durowar da tv yake kai tana juna abun ƙona turaren wuta mai amfani da wuta ( electric burner wanda a lokacin batai yawa ba, sai gidan ƴan gayu ake iya ganinta) "Anty Hadiza, Mama ga Anty Hadiza " Cewar Sailuba kenan. Maman ta ɗago da dariya tace. "Uwargida sarautar mata ke ko me kike yi a nan sassafe kamar wacce tayi ɓatan kai?" Hadiza dake ta kallon falon kamar ta wanke makanta tace. "Ke dai Anty Bari. Kinga rushi nazo ɗiba inaso kafin in karya in kunna turaren wuta" Sai Anty Badi'a tayi Dariya tace. "Ina zuwa. Sailuba ki zuba mata farfesun kan ragonnan a ƙaramar kula maza" Ta shige ɗaki sai gata da sabuwar ( electric burner) a kwalinta ta miƙa mata dama guda biyu ta siyo tafiyarsu Umara ita da mijinta. "Ga wannan aita ƙona turare lafiya." Hadiza ta amsa da murnarta taima Anty Badi'a godiya mai yawa. "Na ganki da leshi kina wayayya. Ai leshi kwalliyar dare ce, ko rana. Da safe ai ƙananan kaya ya kamata ki mayar su zama ababen sawarki. Karfa ki ba damu yarinya ƙarama ta ciri kambu" Hadiza ta zaro idanunta waje tace. "Nifa Anty ƙananan kaya guda ɗaya jol gareni. Wata rigace doguwa mai hannu ɗaya. Itama ƙawatace ta kawo mun. Ina dai da rigunan bacci" Miƙewa Anty Badi'a tayi tace. "Jira" Bata jima ba sai gata da leda ta miƙo ma Hadiza. "Kije maza ki sake kayan jikinki ki sa wannan. Zuwa anjima Sailuba zata zo ta kira mun ke. Akwai Hajiyar da nake siyayyar ƙananun kaya a hannunta kayanta suna da kyau Dubai take siyosu. To anjima dama zata kawo mun kaya, da ƴan sabulan gyaran fata." Cikin murna Hadiza ta fito tana shima Anty Badi'a da albarka. Koda ta fito bata ga Innar Khadija ba, ta ɗebi gaushinta ta wuce. Tana kunna turaren wuta ta shige ɗaki ta buɗe ledar da Anty Badi'a ta bata. Riga da sikert ne irin na jikinta sak kalace ta bambanta. Na jikin Anty Badi'a siket ɗin mai ruwan gorrone, sai rigar mai ruwan madara da kwala a wuyan rigar. Ita kuma Hadiza nata siket ɗin kalan jinin karene maron sai rigar mai ruwan madara. Ta saka kayannan yayi ɗas a jikinta rigar ta ɗan matseta dan tafi Anty Badi'a cikar ƙirji. Tana gyara gashi ta jiyo sallamar Shafa a falo. Shi kuma gogan naka masu abu da abunsu sai ya kutso kai ya shigo cikin uwar ɗakin. Ƙur yayi mata da idanunshi yana mata wani mahaukacin kallo mai ɗauke da guguwar sha'awa da burgewa a ciki. Manna ƙirjinshi yayi a nata ƙirjin, yayi lub a jikinta yana shaƙar ƙamshin dake saurin tayar mishi da jarabarshi. Ajjiyar zuchiya Hadiza ta sauke. Gwadabe ya ɗago idanunshi da suka sauya kala yace. "Wallahi kinyi kyau sosai. Kayannan ya amshi jikinki da fatarki ƴar duma_dumata" Murmusawa tayi wani farin ciki ya baibaye zuchiyarta. "Nagode ango mijin Amarya. Naga sai sheƙin angwanci kake yi." Murmushi yayi mata dan yaji sautin kishi a muryar tata. "Shafa tana falo kizo muci abinci." Da sauri ta kalleshi tace. "Abinci kuma, a ina za'aci abincin ba'a ɗakin Shafa kake ba?" Dariya yayi mata. "Abincinne nace ta ɗakko muzo muci a nan ɗin. Hakan nake so mu dinga yi, sabida zai samar mana nutsuwa da fahimtar juna. Wacce bata da kwana ma zata samu damar zantawa da mijinta. Muje ko?" "Amman Yaya Gwadabe" "Shishshsh... Bana son kice komai, kizo muje" Ba dan ran Hadiza yaso ba dai. Tayo jigum har Gwadabe ya fice tana tsaya tana tunanin ta ina wannan lamarin zai soma. Yama za'ace wannan tsarine me kyau. Me yasa wacce take da miji ba zata zauna ita kaɗai da mijinta ta samu nutsuwa su ciyar da juna abinci a baki cikin shagwaɓa da soyayya ba? Ɗan guntun tsaki ta yi kana ta fito rannan nata a mugun ɓace. Ɗakin ya cika dam da hayaƙin turaren wuta ko ina yanata bulbula ƙamshi masha Allah. A gefe guda ta zauna tana fuskantarsu tare da ƙarema tiran abincin Shafa kallo. Itama Shafar ita take kallo tun futowar tata. Sanye take cikin riga da zane na atampa ɗinkin wasila. "Yaya ina kwana, an tashi lafiya?" Kallon Shafa tayi sai ta saki fara'a a zahiri, a baɗini kuma ji tayi kibiyar kishin Shafa ta soki murfin ruhinta. Gani tayi a idanunta shafa tayi kyau kaalar atampar ta amshi fatarta, sai kishi ya bijiro mata. Ta bangaren Shafa ma fitowar Hadiza saida ya faɗar mata da gaba, take ta raina kwalliyar data kashe minti talatin tanayi. Kuma ƙamshi Hadiza ya goge tarihin turaren akwati data fesa ta fesama Gwadabe ma. (Ire_iren wannan ke hana zaman lafiya a tsakankanin kishiyoyi. Shi yasa akeso mace ta yarda iya wuya tafi kishiyarta. In tasa hakan a ranta ta huta da kaso hamsin. Muddin duk abinda zai faru kina hango cewar an fiki, to akwai matsala. Anya gidan Gwadabe zai zauna lafiya kamar yadda yake tunani kuwa. Mu dai je zuwa mahaukaci ya hau kura) "Lafiya lau Amarya. Mai gida takobin yaƙi ina fatan kabi da'ita a hankali kaga yarinyace kuma kai ɗin baka da dama" Ta ƙarashe zancan da wata mayaudariyar dariya mai sukurkuta kan mai gida. Sai murmushi yayi dan shingin kaɗanma ya ƙware da tean da Shafa ta zuba mishi yana kurɓa. Dariya kawai yayi, ita kuma Shafa kunya ta mamaye illahirin jikinta. Taliyar Hausa ce da miyar stew ta zuba musu ta caɓa miyar akai sai ruwan bunu mai citta. A plate ɗaya ta zuba ta saka cokula uku. Murmushi Hadiza tayi tace. "Ayya ai da baki zuba dani ba. Kinga abincin karyawata na riga dana kammala." Kallonta Gwadabe yayi bayan ya kai lomar taliyar bakinshi. "To ba sai mu haɗu muci duka ba Hadiza. Ita Shafa ai ba zata ji daɗi ba in baki taɓa abincinta ba." Ɗan gajeren murmushi tayi tace. "Shafa zuba mini shayin in sa albarka. Doyar na tashi ina sha'awar ci, dan da zazzaɓi ma na tashi" Kalmar zazzaɓi ne yasa Gwadabe ya sarara baice da Hadiza uffan ba, duk da yasan lafiyarta ƙalau abincinne ba zata ci dasu ba kamar yadda tayi rannan. Doya da farfesun ta raba biyu ta ajjiye musu rabi, ta soma cin nata. Ɗakin yayi tsit baka jin motsin komai saina lokula da tauna. Su ukun duka ko wanne da abinda ke ƙunshe a ranshi. "Hadiza kece babba ina mai ƙara baki haƙuri dan Allah ku daure ku wanzar da farin ciki a wannan xamantakewar. Kunga ni a zaman da nayi da uwar ƴaƴana bamu taɓa samun saɓanin da har za'ace mun kwana muna rikici, ko gaba da sauransu ba. To ina fatan kuma zan sameku kamar Iyabo, koma fiye da ita dan a zahirin gaskiya Iyabo mutum ce guda da ɓari. Ina fatan mu zauna Lafiya " Take kishin Iyabo ya turniƙe Hadiza ta yanda ya kusan rufe mata idanunta tayi ɓaranɓarama. Allah ta ambata a zuchiyarta taja bakinta ta yi shiru. Abincin dake gabanta ma rufewa tayi dan sai taji bakinta na wani irin ɗaci. A cikin zuchiyarta tace. "Niko zanso ganin wannan Iyabo ido da ido inga me ta mallaka wanda yayi tsaye cak a zuchiyar Gwadabe da har mu yake ma ishara da muyi koyi da ita wajen kyautata xamanmu a tsakaninmu dashi " "Bakice komai ba ke Hadiza " Gwadabe ya katse mata zaren tunaninta. "Allah ya bamu ikon haɗe kanmu mu baka nutsuwa" A haka dai suka kammala cin abincin Shafa ta soma kwashewa. "Meye ya ɓata miki ranki haka Hadiza. Wai me yasa kike yin hakane Hadiza ta? Haba gimbiyar mata tauraruwar zuchiyar Gwadabe " Harara ta watso mishi tace. "Iyabo tana numfashi na zama tauraruwar zuchiyarka?" Dariya yayi kafin yace wani abu Shafa ta shigo. Dole shima ya miƙe yai mata sallama ta bisu da idanunta sai ga hawaye sirara sun zuraro mata. Da sauri ta share hawayen nata ta miƙe ta soma gyara wajen da akaci abincin, duk da dai ba datti a wajen. Sallamar Ine Hadiza ta jiyo daga ƙofar ɗakinta. "Ah su Ine manya kune a gidan sassafe?" Zama Ine tayi tace. "Ke dai bari yanzu na shiga cikin gida na tarar da Malam na rikici da Baba Suwaiba, da Amaryar Malam. A taƙaice a kan idanuna duk Malam ya koresu sun fice da akwatunansu. Gaskiya ban taɓa ganin ɓacin ran Malam irin na yau ba." Daɓas Hadiza ta zauna a kujera. "Malam ya koresu fa kika ce, to me suka yi haka?" "Tabb wallahi ban sani ba, kinsan Baba ba faɗamun zata yi ba kona tambaya. Ni ban tambaya ba. Babace tace in koma gida kawai, shine nace baro in shigo mu gaisa zan shiga wajen Anty Badi'a ma" Hadiza tayo jigum kana tace.." "Zanga sanda gidanmu zai daidaita. Kishine ko wacce ya cika mata ranta fal. Amaryar Malam na jima ina ɗauke da cikinta ba dan tana cin albarkacin mahaifina take aureba da tuni ta gane kuranta. Sabida tana da fitina da yawa fiye da sauran iyayen namu." Nan dai suka ɗan taɓa hirarsu Ine tai mata sallama ta tafi. Sai wajajen azahar Sai ga Sailuba tazo kiranta. Wayarta ta ɗaga ta kira Gwadabe ringing biyu ya ɗaga. "Gimbiya lafiya dai ko?" Murmushi tayi tace "Lafiya lau. Dama Anty Badi'a ce tace tana son ganina shine nace bari in sanar maka" Sai da yayi murmushi yace. "Masha Allah kije ba damuwa. Ni bana gidanma muna wajen Malam, an ɗan samu kacaniyane a cikin gidan. Sai dai inna dawo zakiji komai" "To Shikenan saika dawo ɗin." Wayarta ta kashe suka fito ita da Sailuba. Su Yaya Jazuli da su Nazifi suna ɓarayin Yaya jamilu. Suma zancan korar mahaifiyarsu da Malam yayi a gidan suke yi. Karaf a kunnen Hadiza Nazifi yana cewa. "Dole zamu je mu dawo da uwarmu babu inda zata je, tunda ta haifemu muna da gado a gidan" Hadiza ta kalleshi shima ya kalleta yana muzurai. "Dena kallona dan ta abu kazan..." Ya danno wani zagi ya dannawa Hadiza tare da ɗorawa da cewa. "Ku gaku ƴaƴan so, yaran mowa shafaffu da mai. To wallahi wannan abun masifa da bala,i kawai zai haifar dam mahaifiyarmu ba zata koru ba" In kun tanka Hadiza ta tanka. Inda sabo ta saba da jin waɗannan zagi da waɗannan furuci na cewar sune ƴaƴan so a idanun Malam. Haka zalika dukkan abinda ya faru a wannan gida nasu gani akeyi dasa hannu Baba Fhatsima da Yaya Tasi'u da suke ganin kamar suke juya Malam. Hadiza ta shiga tunanin yanzu haka suma in suka ƙi samun zaman lafiya a tsakaninsu yaransu zasu taso a cikin ƙiyayyar jininsu? Wai to wake da Matsala ne mazan dake auro matam su haɗe su. Ko kuma matan da aka aurone masu matsalar? Ita dai tasan matsalarta ɗaya kishine, kuma kishi shine matattakalar data rusa ahalin gidansu da duk gidajen da aka kasa samun daidaito da fahimtar juna kuma ba mace ɗaya bace a cikin gidan. Duk kishi shine sababin dake sa uba ya tsani ƴaƴan cikinshi, uwa taji kamar ta kashe ɗan da kishiyarta ta haifa, kishiya da kishiya su kasa samun zaman lafiya. Gida ya zama gidan rikici da hayaniya kullum. Wannan lallai babbar matsalace da Hadiza take ganin bai kamata ta bari sheɗan yaci galaba a kanta ba. Take zuchiyarta ta sassauto mata dangane da zafin kishin Shafa. Duk da bata da burin yin zaman doya da manja da Shafa. Amman ta ɗaura ɗamarar saita zama tauraruwa sarauniya a birnin zuchiyar Gwadabe ta yanda zata ture har matsayin da Iyabo take dashi. Da wannan tunani ta shiga falon Anty Badi'a. Suna zaune a ƙasan kafet an barbaza kayayyakin mata na ado da kwalliya kyawawan gaske Anty Badi'a sai ɗagawa take yi. Hadda manyan zannuwan gado ƴan kwali irinna saudiyya ɗinnan masu laushin gaske. "Kinga yadda kayannan suka amsheki kuwa Hadiza? Ga wasu samfurin masu wando, da gajeren siket an kakkawa zo zauna." Cewar Anty Badi'a. Zama Hadiza tayi da hanzari suka soma ɗaɗɗaga kayayyaki harda wasu rigunan bacci na garari . "Kinga zaɓi kaya Hadiza. Ba'a bori da sanyin jiki. Kinga waɗannan dana zaɓar mana ni dake, duba kiga kalolin sunyi" Anty Badi'a ta miƙo mata kayayyakin ta soma waresu tana gani, dogayen ruguna, da riga da wandone, sai kuma mai gajeren siket wanda zaka saka daga kai sai mijinka. Kaya dai kusan guda takwas_takwas harda zanin gado na kwali mai ɗawisu irin na da. Hadiza rabin kuɗin kayannan ta biya, Anty Badi'a ta biya mata kuɗin rabin. Ta sake yin mata kwalimar nata ƙananun kaya. Ta bata wasu surruka masu ƙarfi tace ta riƙesu tayi amfani dasu zata ci ribar zaman Aure. "Fatanmu shine mutuwa itace zata rabaki da mijinki. Kinga maza kullum su babban birinsu shine mace ta zama musu tamkar hawainiya wajen caccanja salo_salo na komai nata ta yanda zamanku bazai zama ya gundureku ba. Ki tabbatar a ranar dazai bar ɗakinki kin mishi abinda zaiji yana ɗoki da mararin sake shigowar girkinku. Ki riƙe talaucinshi kuita mishi adda'a Allah zai buɗa mishi Gwadabe yana da zafin nema ba malalaci bane muna mishi fatan nasara. A ido haka Shafa bata da wani matsala kiyi ƙoƙarin janyo ta a jika, karki bari wasu daga cikin gidan su janye miki ita da hakanne gulme_gulme ke ratsowa. Hadiza ai Baba ya kamata ta zame miki allon kwaikwayo. Dan har gobe kinga yadda ruwa yake maganin dauɗa. Anty Badi'a ta jima tana bawa Hadiza surrukan da zasu tallafi zamantakewarsu daga ƙarshe sukai sallama Hadiza ta koma ɓarayinta. Gaga gaga haka rayuwa taci gaba da matsawa, duk safiya da irin shiga da Hadiza take yi na alfarma, ga ƙamshi. Itama fa Shafa bawai a baya aka barta ba itama tana yin nata salon kwalliyar, amman ita tafi ganewa atampa, leshi sai dogayen riguna ƴan kanti. Itama suta riƙe a matsayin makaminta. Ko wacce cikinsu rigegeniyar take yi wajen ganin ta zama ta gaban goshi. Rayuwar gidan babu daɗi domin kuwa wasu basa ko ga miciji da wasu. Ko wanne ƴan ɗaki isu_isu da matansu suke mu'amala, gaisuwa wannan bata shiga tsakani. Shi yasa tsakaninsu Hadiza da matan su Auwala ne kawai suke mu'amalarsu a tsakaninsu, sai Yaya Tasi'u daya zame musu garkuwa. Ko wacce in zata fito bata da aiki sai waƙe da habaice_habaice. Sai gasa da hassada ta shigo cikin lamarin. Daga masu suyan kifi, sai masu suyan nama, ko kaza. Ga gasar sutura da kwalliyar safe data yamma dan tarbar miji." Ta bangaren gidan Malam kuwa rikicine ya ɓalle ƙaramar maganace take son zama babba. Iyayen matanshi daya tura gida sunyi jelen har sun haƙura. Amsa ɗaya malam yake faɗa musu itace "Su je su huta a gidajen iyayensu. Nima inaso in huta" Yaran Baba Suwaiba suka haɗe kansu suka samu Malam akan batun gyatumarsu. Suma Malam ya fatattakesu da zancan. Bayan kwana uku suka je suka dawo da Babarsu gidan. Ranar sunga tsiya. MRS BUKHARI Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 *INA MASU SAN SIYAN KAYAN ƘAMSHINA? NESA TAZO KUSA ZAN TURO DA KAYA KANO DAGA KANO ZA'A TURA MIKI DA KAYANKI DUK GARIN DA KIKE, IN A KANO KIKE KAYANKI HAR GIDA ZAI ISO MIKI IN SHA ALLAH. KAYAN ZASU ZAUNA A HANNUN ANTY ZEE MUSA COLLECTION DA IZININ ALLAH KAMAR YADDA AKA SABA. IN KINA BUƘATA KIYI MAGANA A HAƊO DA NAKI KAYAN HAJIYA* *ƳAN PROMO SUMA SU SOMA TURO DA KUƊIN PROMO ƊINSU. 10k NE ABU UKUNE A CIKI. IYAKAR NA MUTUM HAMSIN ZAN HAƊA MASU SO SUYI MAGANA KARKU BARI WANNAN PROMO YA WUCEKU* *WAƊANDA SUKA SAN KAYAN PROMO NA NASAN BABU WASA. IYAKAR MASOYANA NE KAWAI PROMO DINNAN BAZAN SIYARMA DA NA WAJEN GROUP BA. KAYAN 20K NE NA BAR MUKU A 10k DOMUN KU DA BAKU TAƁA AMFANI DA KAYANA BA KU JARABA* *WAƊANDA KUƊAƊENSU YAKE HANNUNA DUK ZAN SALLAMEKU SANNAN AKWAI KYAUTA DA ZAKU SAMU IN SHA ALLAH.* *WAƊANDA BASU TAƁA SIYAN KAYAN ƘAMSHINA BA SUMA AKWAI KYAUTA TA MUSAMMAN DA ZAN BAKU IN SHA ALLAH.* NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 20 "Wallahi Suwaiba ba zata shigarmun gidana ba, tunda ba da kudinku na gina gidan ba. Ki koma gidanku ki huta, kinganni hutu nake buƙata ni kam" Cikin marairaicewa Baba Suwaiba tace. "Haba Malam ai in adalcine sai ka sallami matan naka duka, bamu ka waremu ba su ka barsu ba. Sannan Malam wanne irin haƙurine daga gida ban turo an baka ba ne? Sagiru kasa baki" Ta dubi Sagiru halamar agajinshi take nema. Dan dama yafi kowa rashin kunya a cikin gidan. "Baba muje ki zauna a ɓarayinmu, mun riga mun ɗakkoki daga gidanku ai ba kya koma ba. Muje kinji ki dena damun kanki" Ya kinkimi akwatinta ya kaita wajen Amaryarshi yace ta zauna na wani lokacin. Haka kuwa Baba Suwaiba taci gaba da zaman takura tana kwana a falo akan doguwar kujera. Kwananta biyu ƴarta ƙanwar Sagirun Aisha tazo ta ganta, ta tattageta zuwa nata gidan tunda su suna da estira ɗakin da zata zauna ita kaɗai. Amaryar Malam kuwa tana gidansu zaman gidan babu daɗi, gashi mahaifinta yace shi ya gaji bazai sake zuwa ba Malam hakuri ba. Wannan lamarin ya sake farraƙa kan gidan Malam. Bayanin da Baba Fhatsima take ta yi mishi kenan babu dare babu rana kan hakan ba ɗa mai idanu zai haifar ba. Shi kuma yace ta zuba mishi idanu data matsa sai cewa yayi. "Fhatsima in kika matsamun akan batun su Suwaiba, to zaki sa in sallamesu gabaki ɗaya su fice mun a gida. In yaransu zasu bisu duk su haɗa dasu. Ina amfanin yaran da basa dajarta ubansu ne?" Dole haka Baba Fhatsima ta tsuke bakinta tayi shiru. Da Baba Asshi da yaranta sai suka shafama kansu ruwa, dan basa fatan uwarsu ta bar ɗakinta azo ana roƙon Malam yana botsarewa. Wannan kenan" Yau monday tushen aiki. Ayau Angwaye zasu koma bakin aikinsu kasancewar yau satinsu guda tim da tarewa a ɗakunansu. Wanda yayi dai_dai da kwanan Gwadabe huɗu a ɗakin Shafa. Tun asubar fari Gwadabe ya hura huta ya ɗaura ƙatuwar tukunyar maganinshi, yana dawowa Sallah ya sauketa. Shafa ta juye mishi ruwan wanka, shi yana shirin fita kasuwa ita kuma ya kwatanta mata yadda zata ƙulla mishi maganin nashi. Tana girkin safe tana ƙullin magani. Gwadabe shi kuma ya shirya tsab cikin kayan nema ya fito ya kama ɗaurin magani. Ita kuma Shafa ta samu damar kammala haɗa kayan karin kumallo a babban tire, ta shiga ban ɗaki ta watsa ruwa. Cikin kanƙanin lokaci ta shirya cikin doguwar rigar shadda mai ruwan ƙasa tasha surfana. Tana fitowa Gwadabe ya kalleta yace. "Kinyi maƙurar kyau Shafa. Ki kai abincin ɗakin Hadiza nima ganinan" "Godiya nake yi mijina na kaina" Murmushi yayi mata yana son sanyin halin Shafa sosai. Tiran ta ɗauka ta shige ɗakin Hadiza, bayan matar Sabitu ta ja dogon tsakinta. "Gwadabe kayi da jiki bakwai harta gota, Mammada fa harya fice yana jiranmu a ƙofar gida, kai kuma naga sai yanzu ma zaka karya" Cewar Auwala daya fito cikin shirin fita kasuwa" "Bari kawai in musu sallama sai in fito mu tafi. Ko ƴar tsala naci acan in munje." Miƙewa Gwadabe yayi tsaye da sauri. Bokitin maganin ya kinkimo ya fito dashi tsakar gidan, ya ajjiye tsumman da yake gammo dashi, ya samesu a ɗakin Hadiza. Itama Hadiza taci ado yau da Atampa riga da zani, jakarta da mayafinta yana gefenta itama hutun da makarantar su ta bata ya ƙare yau. "Barka da Safiya yallaɓai, lafiya ka tsaya a kanmu sai binmu da kallo kake yi?" Cewar Hadiza da take magana a ɗan shagwaɓe. Yana matuƙar jin daɗin shwagwaɓar Hadiza da yadda take taimakonshi akan shimfiɗa wajen tayashi cimma manufa. Saɓanin Shafa da take kwanciya kamar ruwa sai inda aka juyata" "Kunyi kyaune. Nake mamakin ni Gwadabe mahaƙin gwal, mai saida maganin basir nine da mata fella_fella haka? Allah nagode maka. Kuyi haƙuri abincinnan bazai ciyu ba. Su Auwala ni suke jira, saina dawo zanci abincin acan. Hadiza yau zaki koma bakin aikinki kema ko?" "E hakane. Ni kaina jiranka nake yi dama ka shigo in muku sallama, inna tsaya yin breakfast a gida zanyi latti. To acan nake karyawa ina tafiya da filas ɗin tea da abinci" "To Shikenan tunda Hakane. Na soke karyawar safen. In yaso da daddare ma dinga haɗuwa, ni na tafi. Shafa ki yi haquri ki koma ɗakinki da abincin" Sam Shafa bata ji daɗi ba. Tana lure dama Hadiza bata son cin abincinta, kuma ita ta duba ta hanga bata ga ta inda Hadiza ta fita tsafta ba. Ba dai tasan irin daɗin girkinta ba wannan, tana jiran ranar girkintane taci taji" Tiran abincin ta ɗauka. "To Yaya sai kin dawo" Tasa kai ta fice. Tana fita Gwadabe ya jawo Hadiza dake tsaye jikinshi, ya cusa kanshi a kirjinta yana ajjiyar zuchiya. "Uwargida a matse nake dake fa sosai. Ina mararin juyowar girki bazan ɓoye miki ba" Idanu ya lumshe yana hasaso daren ƙarshe da yayi a ɗakin Hadizan. Murmushi tayi mishi tace. "Kamar yaune lokaci zai zagayo, harma ya wuce. Haka zakaita zagaye har abada, tunda burinmu mu dauwama tare da kai har abada" Ba shiri dole ya saketa ya fice, ta biyo bayanshi suna dariya. Gwadabe ya suri bokitin maganinshi ya fita. Auwalane ya ɗaura mishi aka suka nufi hanya, Allah cikin ikonshi kafin su isa inda zasu hau abun hawa Gwadabe yana taɓa ciniki babu laifi. Acan inda ake aikin haƙon zinare kuma tas maganinshi yake ƙarewa sakamakon maganinshi yana da kyau, kuma masu saye sun shaida yana musu aiki. Gashi yana gaba_gaba wajen haƙon zinare, Gwadabe namijine mai zafin nema da zafin nema babu wasa a lamarin aikinshi. Haka rayuwar dai taita garawa yau mun wayi gari Gwadabe ya gama kwananshi na ƙarshe a ɗakin Shafa, ya fita da safe inya dawo a ɗakin Hadiza zai ya da zangonshi. Sannan yana fitowa Yaya Tasi'u ya bashi takaddar samun aikin Shafa, a wani asibiti zata dinga ba da kati. Gwadabe yayi murna sosai kuma ya yaba da ƙoƙari da kulawar Yaya Tasi'u gaya. Mutuniyarku Hadiza yau wayar garin tayi tamkar anyi mata bushara da gidan aljanna dan daɗi. Tana cikin farin ciki ta tafi makaranta. Hatta ƙawayenta malamai sun gano farin cikin da take ciki. Sadiya uwar zolaya, bayan Hadiza ta fito daga aji ta dawo ofishin malamai dan tanaso ta karya kafin lokacin komawarta wani ajin yayi tace. "Waini Hadiza ko Gwadabe yayi muku wata gagarumar kyautace yau ɗinnan? Hatta kwalliyar da kika caɓa naga ta dabance, harfa taku kika canja." Dariya gabaki ɗaya matan cikin ofishin suka saka. Hadiza saida ta tura wainar ƙwai bakinta kana tace. "Sharri dai da sa ido Chima in ba haka ba wacce canja tafiya nikam zanyi? Kawai dai yau nice da girki shine naketa nishaɗi. Kuma inata tunanin wanne irin abinci zan tari Oga dashi, tunda mu kai aure baici abincina ba, in banda farar shinkafa dana dafa muka ci da Miyar da Balaraba ƴar ƙanwar Baba ta soya. To Ku bani shawarar abinda zan girka, da irin wankan da zan fella Sadiya kune masu kishiya, bani labarin yadda kike tashin kan abokiyar zamanki ran girkinku?" Wata dariyar mugunta Sadiya ta shiga yi har tana tuntsurawa. "Wallahi har kin tuna mun da Safara'u. Ranar girkina sam bata da sukuni, kalar tausayi take zama. Gashi Sanusi shi ƙa'idarshi a turakarshi muke zuwa cin abinci. Gaskiya kusan kullum da jan idanu take fita in ranar girkinane" Hadiza tayi shewa tace. "Shegiya ƙawata. Bani sirrin mana nima in ƙara da nawa. Kinsan Allah inason mijina sosai, kuma in na kalli Shafa a kullum sai inji kamar ma in shaƙeta uban kowa ya huta. A kallon da nayi mata lokacin biki, banyi tunanin zafin kishina zai iya sauka a kanta ba, danni na raina yanayinta kuma nasan ƴar ƙauyece duk da tayi karatu. Ashe wallahi kallon tsoro nayi mata itama akwai kaya. In ta shawo wankannan suka shigo mun ita da Gwadabe kuma naga hankalinshi a kanta. Kinsan Allah kamar in zazzagama kaina fetur in ƙone haka nakeji dan kishi." Dariya suka kwashe dashi. Barira tace. "Ni uwargidanmu batta da son girma amman bata da damuwa. Amman Nabila itace take neman ɗauramun hawan jini a baya. Sai da Sadiya ta bani maganin damuwar da Nabila ta so ɗauramun. Shawarwarine nagartattun da dabarun yadda zaki zama wata ta daban a zuchiyar oga, da kissar danne kishi. Kinga da ɗan abu kaɗan Nabila zata yi, kawai sai inji kishi kinsan Allah bana sanin sanda nake lailayon mata uwar ashariya. Kinga ina girma a wagga lamari?" Dariya suka kwashe dashi. Ƙararrawa aka buga dole Hadiza na jin daɗi ta tafi aji dan ba yara darasi. Data dawo suka ɗaura, Sadiya ta zauna ta karanto mata abubbuwa masu girman gaske ( Sannu a hankali zaku jisu a aikace cikin labarin) Waɗannan maganganu su suka sake buɗe kan Hadiza tayo farin ciki gaya. Ana tashi ta wuce wata ƴar ƙaramar kasuwa dan yin cefanen naman rago ta siyo, sai bushasshen kifi, da cefanen tumaturi da su tattasai, attaruhu. Albasa an kaita dashi kusan rabin bihu ma. Sai kankana kwallo daya da lemun tsami manya na nera hamsin. A gajiye ta shigo gidan, babu kowa a tsakar gidan ɗakinta ta buɗe ta shiga. Ta ɗan kwanta ta huta bacci ya ɗebeta zuwa la'asar. Da sauri ta miƙe ta fito, daidai Shafa ta fito daga banɗakinta da halamun alwala ta ɗauro" "La Yaya yaushe kika dawo?" "Na dawo bayan azahar, nayi tunanin ko bacci kikeyi shi yasa ma ban tasheki ba ni kam. Kinga bacci nayi yanzu na farka" Shafa tace. "Ai kuwa bacci nima na tashi yanzu. Dan ɗazu naso yin baccin amman an ɗanyi rikici a gidan akan shanya abinda ya hanani baccin kenan" Haɓa Hadiza ta riƙe. "Akan shanya kuma, to dawa dawa su kai faɗan?" Shafa tace. "To matar wancan ɗakin na gaba can, da matar ɗakin dake kallo nakine. Sunyi faɗa sosai harda fashe bokatai fa" Baki Hadiza ta taɓe. "To Allah ya kyauta, bari inyi sallah " Tayi wucewarta banɗaki, Shafa itama ta shige nata ɗakin. Tana idar da Sallah ta sauya kayan jikinta zuwa wata ƴar doguwar riga mai sauƙi haka, ta fito domin soma girki. Matan gidanma kaf ɗinsu suna kitchen anata ɓuruntu. Gida ya kaure da ƙamshi kifine, kazane kowa dai da abinda yake girkawa. Sanwar miya Hadiza ta tsayar. Tana tsintar waken da zata zuba a miyar. Baba Suwaiba ta fito tsakar gidan tana sababin danme za'a hana surukarta shanya. "Ke Fatima ki fito fitsararriya kwashasshiya fito inji me kika taka" A madadin ita ta fito sai Sabitun ya fito da kanshi. Rashin kunya yayi mata, dama basa ganin kowa da gashi a gidan. Nanfa rikici ya ɓalle rikicin da sai da Malam da Baba Fhatsima suka yo tattakin shigowa. Daidai Baba Suwaiba tayi ɗamara ta nufi Sabitu da duka. Malam "Yayi kyau Suwaiba Nagode gaya. Ku kuma duk ku watse ko wacce ta shige ɗakinta. Gobe da safe daku da mazajen naku ina nemanku a gida bakwai na safe. Kai kuma Sabitu sannu da Uwar taka kake sa'insa sabida ɗiban albarka ko?" Iyakar abinda Malam yace kenan ya juya ya fice. Idanu Hadiza da Baba Fhatsima suka haɗa. Ƙunci da damuwa ƙarara a shimfiɗe a fuskar Baba Fhatsima. Kai ta gyaɗa ta bi bayan mijinta. Suna fitowa Baba Suwaiba ta biyo bayansu. Tsautsayi malam bahaushe yace baya wuce ranarshi. Kuma shi dana sani ƙeyace. Malam na ganin fitowar Suwaiba yace. "Na sakeki Suwaiba. Aurena dake ya ƙare, na gaji da baƙin ciki da takaicin da kuke ɗauramun ina shanyewa tsawon shekaru. Zuchiyata tarwatsewa kukeso tayi, ko faɗuwa kuke so inyi in mutu in bar baya da ƙura. To ta faru ta ƙare kije dan kanki." Baba Fhatsima ta dafe ƙirjinta. Baba Suwaiba kuma ta fashe da ihu harda kururuwa. Malam ya tafi ya barsu su biyun a tsaye yana tafe dafe da kanshi da yake jin kamar zai tarwatse. "Ki ƙarama bokanki kuɗi Fhatsima burinki ya idasa cika. A baya har hauka kika sa nayi na fito tsirara. A yanzu kinsa Malam ya sakeni ni Suwaiba. Ki rubuta ki ajjiye akwai ranar ɗaukar fansa tana tafe duk daren daɗewa ni Suwaiba saina saki zubar da hawaye." Cikin kuka take maganar. Murmushi Kawai Baba Fhatsima tayi tace. "Allah ya kyauta. Nasha tabara na sha yasin" "Ki ƙara da amanan rasulu. Fhatsima sai naga bayanki dake da yaranki duka, dani kike zancan" Har Baba Fhatsima ta ƙule Baba Suwaiba na zage_zage. Wannan lamarin ya rura wutar hatsaniya mai girma hatsaniyar da a tarihin rayuwar iyalin malam ba'a taɓa yin irinshi ba. Dan abun yakai harda faɗa da makami a tsakanin yaran Baba Suwaiba da su Auwala da suke kare uwarsu. Baba Fhatsima sai kulleta akayi ita da Malam a turaka. Yaya Tasi'u kuma ganin abun ya wuce gona da iri sai ya kira ƴan sanda aka fita da yaran Baba Suwaiba zuwa police station domin yima tubkar hanci. Malam yana goye da hannunshi a bayanshi sai kai kawo yake yi harda hawaye a idanunshi. Abun a tausayane ace dattijon magidanci yana hawaye ku kanku kunsan abun yakai intaha. Tunaninshi yake mayarwa baya a lokacin da suke rayuwarsu ta talauci da tsantsar soyayya shi da Fhatsima. Fhatsima tayi mishi son da harya koma ga Allah ma bazai samu macen da zata soshi rabin haka ba. Gashi a sakamakon giyar jini a jika da giyar kuɗin da bai taka kara ya karyaba ya ɗebo ma kanshi kara da kiyashi ɗaukar marar sani. Yau shine aka tura a ɗaki ƴaƴan cikinshi na fito na fito dashi kan uwarsu. Fhatsimar daya raina a baya ita da ƴaƴanta a yanzu sune garkuwarshi. Madallah da mace tagari, madallah da uwa tagari. A daren Malam ciwonshi ya tashi bil haƙƙi gaga_gaga aka wuce dashi asibiti. Hankulan kab ƴan gidan a tashe yake gaya. Dan ɗaiɗaiku daga cikin ƴaƴanshi masu mishi fatan mutuwane kawai sukai baccinsu harda minshari. Masu son rayuwar malam sune suka kasa rintsawa har zuwa wayewar gari. IYABO:. Satinmu uku a asibiti. Sai godiyar Allah domin jikin Dada ana samun haske sosai, har hira muna yi da'ita. Da safe da Yaya Hamma ya shigo ya miƙo mun Madara mai zafi a cikin gora. Sai Dada ta dubemu tace. "Hamma ko bayan babu raina Jabu itace matarka. Nayi imanin a hannunka zata samu nutsuwar data rasa a baya. Ina mata fatan samun miji tamkar mahaifinta Adetoye. Mutumne mai yakana wanda yasan darajar mace." Yaya Hamma yace. "Dada ai Jabu ƙanwatace ko bani na aureta ba sai inda ƙarfina ya ƙare a kanta. Wannan aure duk dangi suna farin ciki dashi, Jabu zata dawo cikin danginta." Dan a wannan lokacin labarin soyayyarmu ya bazu, Hama kuma kamar mahaukaciya haka ta zama. Dan soyayyar da muke ma juna ni da Yaya Hamma soyayyace wacce baki bazai iya faɗeba, alƙalami bazai iya rubutashi ba. Idaninmu a rufe suke ruf. Duk wani bugun zuchiyata ankai an kawo da soyayyar Hamma yake bugawa. Shima nunamun kulawa yake yi irin kulawar da banyi zatonta a wajen bafulacan daji ba. Ina ba Dada Madara a baki tana sha kamar a mafarki saina hango Uwani tafe da Saleem Yana biye da'ita har zuwa gadon da muke. Gabanane ya yanke ya faɗi muka ƙurama juna idanu ni da Saleem babu um babu um_um. Kallon kewa da tsantsar so Saleem yake yi mun. Ni kuma ina mishi kallon tausayi da dana sanin saninshi, domin son maso wani babban ciwone, na ɗanɗani ɗacinshi akan Debisi. Saye Saleem yake cikin baƙar jallabiya wacce ta sake bayyana sirrin kyanshi, gemu, ƙasumba, yalwataccen gashin ido haɗe dana gira, da sumar kanshi su suka zame mishi wani irin adon da suka bashi wani kyau me sanyi, rawanine yane a kanshi mai fari da baƙi, sai baƙin agogo a ɗaure a tsintsiyar hannunshi, ƙafarshi saye da baƙin takalmi me kyau, ga ƙamshinshi duk ya cika wajen . Ana cikin wannan kallon_kallo Yaya Hamma ya shigo shi da Baffa Musa. Uwani ta gaishe da Dada tayi mata yaya jiki. Saleem sai sallama kawai yayi mata, shi ba hausaba, Dada ba turanci ba "Jabu baƙi kikayine?" Cewar Baffa. Shi ko Yaya Hamma gaisawa su ka yi da Uwani tunda dama ya santa. Saleem ya miƙo mishi hannu suka gaisa. Cikin harshen larabci Uwani take mishi bayanin Dada ce mahaifiyata, Yaya Hamma kuma wanane, sai Baffa Musa wan Dada. Tsugunnawa yayi har ƙasa ya gaishesu da turanci. Baffa Musa yace. "Jabu wannan ai sai nake ganin ba bafulatani bane kamar Balarabe ne ko, amman ba larabci yake yi ba?" Yaya Hamma na ɗago na duba. Shima ni yake kallo sai naga idanunshi sun sauya launi kamar yasan abinda ke wanzuwa, dan kallon tuhuma yake yi mun. Duk saina ruɗe na dibibice ainun na kasa amsa maganar Baffa sai Uwani ce tace. "E Baffa Balarabe ne daga ƙasar Saudiyya yazo wajen Jabu. To munje can gidan shine akai mana kwatancen asibitinnan muka tawo" Siraran hawayene suka zubo a idanuna dana kalli Yaya Hamma yana tsaye akan ƙafa ɗaya, ƙirjinshi sai hawa da sauka yake yi. Da sauri na share hawayen nawa dan kawar da zargi, ina cikin tsaka mai wuyar fita, bana fatan in aikata abinda zai sosa ran Yaya Hamma. Yana da mugun kishi akan abinda yake so, a bayama da bai kai ga furta mun so ba yayi kishin Debisi, balle yanzu da maganar Aurenmu tayi nisan da ba da ban ciwon Dada ba da tuni ina ɗakina. Baffa Musa ma yace ana sallaamar Dada daga asibiti washe gari za'a ɗaura auren in yaso daga baya in Yaya Hamma ya gyara inda zan zauna na tare. "Yazo wajen Jabu?" Baffa ya tambaya yana jimamin lamarin. Hamma ya kalla shima, shi dai baice komai ba sai idanu. "E Baffa akwai kayanmu ne a hannunshi na sare_saren dana faɗa muku nayo. Uwani kayanne suka iso?" Na tambaya da sauri ina kashe mata idanu. Uwani ta riga tasan me nake nufi sai tace. "Kaya Alhamdulillah sun iso suna Kano a gidana" Shi kuwa Saleem ni kawai yake kallo. Yaya Hamma kuma ya sauke kanshi ƙasa yana kallon ƙafarshi, sai wasa da ƙafarshi dake kan wadda ya tsaya akai yake yi. "Dada Allah ya ƙara sauƙi. Jabu bari mu ganki mana zamu jiraki a waje" Uwani na faɗin haka ta dubi Saleem tace. "Yalla Saleem" Saleem ya dubi su Baffa yace. "Assalamu alaikum" Yasa hannu a ajjihu ya zaro kuɗinsu na Saudiyya masu tsoka ya ajjiye a gefen ƙafar Dada. Yabi bayan Uwani suka fita. Illahirin jikina ni kuma rawa yake yi. Yaya Hamma na duba, ni yake kallo a lokacin idanunshi kamar garwashi ƙirjinshi ya tsananta hawa da sauka, ya riga yasan akwai wata a ƙasa, dan ance marar gaskiya ko a ruwa zufa yake yi. "Jabu kije ki samesu mana kar ki barsu suita faman jiranki" Inji Dada da bata san dawar garin ba. Kofin madarar na ajjiye da jan ƙafa wallahi na fita. Soyayya gaskiya ce, a wannan lokacin na ji haushin Uwani ainun nasan da gayya tayi maganar domin ita tafi sona da Saleem fiye da Hamma. Ina fita na hangosu a zaune a wani benci, nan na nufesu na isa da sallama siririya a bakina illahirin jikina a mace mus. Murmushi Saleem ya sakarmun na farin ciki. A zahirin gaskiya nasan Saleem yana sona, na yarda da girman son da yake yi mini. To amman Yaya Hamma yayi tasiri a rayuwata baki ɗaya, salon soyayyarshi ya wuce salon da zan tsaya kwatantawa, jin sonshi nake yi tamkar mahaɗin rayuwata. "Alhamdulillah nagode Allah buwayi gagara misali daya sake ƙaddara saduwarmu dake IYABO. Haƙiƙa wannan ranar tana da daraja a wajena." Cewar Saleem kenan dake magana da turanci hannunshi a sama halamar roƙo, haka kanshi yana kallon sama. Ni kuma nama rasa ta cewa. Gabana sai faɗuwa yake yi, tunanina da hankalina yana wajen nemo kalaman da zan wanke kaina dasu a wajen Yaya Hamma. "Iyabo gani na biyoki da batun aurenmu. Inaso a gama komai insan inane matsayata kafin in koma ƙasata, dan in tafi ma da iyayena sahihiyar magana" Ya sake dabaibayeni da wannan kalami a karo na biyu. Shirun nawa yayi yawa, Uwani ce ta zungureni na dawo cikin hankalina, na dubi Uwani ta gallamun uwar harara, na dawo da kallona ga Saleem shi kuma wani irin kallon soyayyar gani kasheni yake yi mun. Ƙofar ɗakin majinyata na duba, Yaya Hamma na hango a tsaye ya kakkafeni da idanu. Da yaga mun haɗa idanu sai kawai ya gyaɗa kanshi ya nufi hanyar ficewa a asibitin da wani irin mugun sauri. Ai saina miƙe ina shirin binshi da sauri. Uwanice ta finciko hannuna ta dangwarar dani a bencinnan na dawo na zauna daɓas. "Wallahi Iyabo ki shiga taitayinki akan wannan Hamman naki abu sai kace taliyar Hausa ke ko kunya ma ba kya ji. Soyayya sai kace asiri, irin auren wahala da ci bayan da kike son yi kenan, a irin ƙauyen da ke kikeson kiyi zaman aure kenan a bukka zaku gudanar da soyayyar? Baki da hankali Iyabo wallahi. Hamma asiri ƙila yayi miki in ba asiriba banga dalilin da zaisa ki maƙale mishi irin haka ba. Arziki na kiranki ke kinfi son ki zauna a talauce. Ki tuno da irin bautar da kikayi a tafiyar aurenki na baya. Jibeshi ƙazamin banza sai tsawo kamar taliyar murji amman a haka kike so. Ji wani irin hawa da sauka na iskanci da ƙirjinshi yake yi wai shi mai zuchiya. Ke kuma da kin ɗibi ƙafa zaki bishi mu ki barmu a gantale a zaune ko?." Murya ta sassauto. "Iyabo kiyi haƙuri ki amshi Saleem a matsayin miji, wallahi zaki ji daɗi. Kiyi tunani ni ƙawarki ce. Ko Dada da kikeson ki taimaka ta dalilin auren Saleem zaki fi samun damar taimakonta. Nasan kina da ƙudirin zama tare da ƴan uwanki ko dan gyaruwar addininsu kamar yadda muka tattauna. Amman Iyabo ai zaki iya saka su a makaranta ba dole sai kece zaki koyar dasu yadda zasu bauta ma Allah daidai ba. Ya fa kamata ki duba" ( ku zaɓa mun miji masoya wannan labari. Ku kanku nasan kun shiga cikin tsaka mai wuyar fita ko? Ina kuma gani Iyabo. Sannan kar kuyi fishi dani akan faɗawa son Hamma da nayi. Hamma ya wuce duk tunaninku. Saƙonninku sun iso gareni ina godiya da soyayya. Akwai wata baiwar Allah data bani dariya da take cewa inna auri Hamma ba zasu yi mun adda'a ba sai dai suce Allah shi ƙara. Wallahi nayi dariya sosai. Ku dai ku biyo labarin kuji ) Anan ƙarshen littafi na biyu ya tsaya. Zamu je hutun kwana goma kafin mu ɗaura daga inda muka tsaya a labarin wasafa farin girki. Yanzu wasan ma zai soma 🙏🏻🙏🏻 Duk mai son turare yayi magana dan Allah da wuri *ASSALAMU ALAIKUM* _GODIYA MARAR ADADI A GAREKU MASOYA WANNAN LABARIN_ _NA SADAUKAR DA WANNAN SHAFIN SUKUTUM ƊINSHI ZUWA GA AMINIYATA, SAHIBATA, MASOYIYATA, SURUKATA, KHADIJA MAIDOKI, MATA A WAJEN PRINCE, ƳAR GABAN GOSHIN YARIMAN MIJINTA._ ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MIKI A DUK INDA KIKE NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE LITTAFI NA UKU GAWURTATTU UKU NA BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI SHAFIN FARKO (1) IYABO:. "Iyabo da wuya ta kasheki gara daɗi ya kasheki. Ki tuno da irin taimakonmu da Saleem yayi mana a lokacin da muke da buƙatar taimakon . Dubi Ahalinshi yadda suka karɓeki duk da kina matsayin baƙar fata, beyerabiya. Ki duba kuɗi da Saleem ya kashe miki. Kayanmu gashi sun iso suna gidana. Ki duba Saleem ya baro ƙasarsu yazo gareki Iyabo. Irin sakayyar da zaki mishi a ƙasar taku kenan?" Uwani ta ɗaureni tamau da dukkan jijiyoyin jikina. Illahirin jikina a mace yake murus. Gaskiya Saleem bai cancanci irin wannan tarbar daga gareni ba. Ɗan murmushi nayi na dubeshi. Ya riga da ya gane akwai matsalane, dan yanayinshi ya sauya, jikinshi kuma yayi sanyi. "Zuwana ya haifar da matsalane Zauja? Ya tambayeni da larabci. A'a Saleem. Ya hanya ina fatan kazo lafiya?" Murmushi yayi tare da sauke ajjiyar zuchiya har yana dafe saitin zuchiyarshi. Hararata Uwani tayi, ta miƙo mun wata jakar kwali wadda sabida ruɗu ni ban ganta tare da jakarnan ba sai yanzu. "Gashi wannan tsarabarki ce daga surukarki" Fizgewa nayi dan a wuya nake da Uwani. Dariya tayi kawai tace. "Iyabo kenan. Baƙin halin naku na yarbawa masu kwalo_kwalo ya motsa kenan?" Banza nayi mata, na mayar da hankalina ga Saleem tare da yi mishi godiya da tsaraba, na tambayi lafiyar mahaifiyarshi da danginshi duka. "Duk suna lafiya kuma sunce a miƙo miki saƙon gaisuwarsu gareki. Kuma sunyi mun fatan nasara. Meke damun Mamane haka, sannan me yasa aka kawota wannan asibitin, kuma ɗakin duk mutane." Ɗan murmushi nayi. Duk wannan abun fa hankalina yana ga Hamma. Babu komai asibitin yana da kyau. Kuma jikinta ya warware an kusan a sallamemu mu koma gida in sha Allah." "To Shikenan zanje in yi sallah inna dawo sai mu tattauna, kuma a gabatar dani ga magabata ayita ta ƙare ko zan samu nutsuwar zuchiya." Kwatancen hanyar da zaiga masallaci nayi mishi. Yana tafiya na dubi Uwani nace. Yanzu Uwani yaya zanyi? Ni da Hamma lokaci kawai muke jira, ina tabbatar miki da ba dan ciwon Dada ba da yanzu wata maganar akeyi ba wannan ba. Wallahi Uwani ni zuchiyata tafi nutsuwa da Hamma fiye da Salim batun ƙauye ko ƙauyanci kuma ni naji na gani zan rungumi aurena in zauna a ƙasata ni yafi mun rufin asiri. Ki tuno irin baƙar azabar da muka sha a hannun larabawa. Shi Salim ɗinnan kinsan mazinacine gangaran, tantirin mazinaci ma kuwa, dani dake da Faty duk fa mun sani. To ina sane bazan auri mazinaciba, ni abun hannunshi bai tsole mun idoba, Uwani kiyi tunani. Zina yaɗo take yi ta lashe zuriya, ki duba mazajen larabawa da yawansu kamar Ayu suke dan tsabaragen son mata" Jim Uwani tayi can ta dubeni tace. "Yanzu ke dai kinji kin gani Hamma dai kike so zakiyi haƙuri da duk abinda in kika shiga zaki gani, shin tunda kin kawo hujjojinki na ƙin auren Saleem shin Iyabo me zai hana ki nutsu ki yi kasuwancinki da sannu Allah zai ɓullo miki da wani, shin ko a matse kike?" Sosai kuwa, muna fatan ganin alkhairi. Nifa na tsorata da sha'anin larabawa ko karen hauka ya cijeni bazan auri Salim ba. Uwani ki mishi bayani an riga an haɗani auren zumunci da ɗan uwana wanda suka gaisa saura sati ɗaya ma ayi bikin in samu mu rabu lafiya" Mun daɗe muna tattaunawa, Uwani ta jima tana bani baki akan nayi nazari kafin yanke hukunci. Ita a tunaninta dan gudun dana sani. Ni kuma babu dana sani a soyayyata da Hamma. Har Salim ya dawo bamu tsaida matsaya ba. Ciki na shiga na kawo mishi madarar shanu a gora yasha sosai sai santi yake yi mana. Uwani ce ta nutsu ta soma yi mishi bayani da larabci kasancewar ta fini ƙwarewa a yaren. Salim hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba har ƙwalla saida ya zubar wallahi. "Allah shine shaidar son da nake yi miki. Ni nasan harda tsoro yasa kika ƙi aminta dani Iyabo. Yaya zanyi da sonki, kinsan sonki zai iya zautani kuwa?" Wasu siraran hawayene suka gangaro a kumatuna. Salim duk ya birkice abinka da farin mutum har fuskarnan tashi ta Zama jawur da'ita haka ma idanunshi. Salim kayi haƙuri bazan iya saɓa ma iyayena domin faranta nawa ran ba. Yayana suka zaɓa mun. Ina mai baka haƙuri , Allah ya ɓillo maka da wacce ta fini alkhairi a rayuwarka da addininka. Na yaba nayi godiya da soyayyarka a gareni kayi haƙuri " murmushi yayi mun yace. "Ina sonki Allah. Amman na haƙura har ga Allah kuma ina roƙon Allah ya baki zaman lafiya da mijinki ya baki zuriya ɗayyiba. In na haifi yarinya zan saka mata sunanki Iyabo" Sai zuchiyata naji ta tsinke ainun. Babu shiri hawaye ya shiga gudu a kumatuna. Billah da zan iya amsar son Salim da zan amsa. Amman kash ko wacce zuchiya da abin sonta, kuma ko wacce ƙwarya tana da abokin burminta. Jabu zaka saka ma yarinyar taka. Sunana kenan ta ɓangaren mahaifiyata." Dariya yayi yace. "Jabu what a nice name" Miƙewa yayi tsaye hannayenshi a cikin aljihun jallabiyarshi yana kallona yana nazartata, ko kuma karanta wasiƙar jaki. "Zan koma Kano. Jibi zan koma inda nafi wayau. Zaki ga saƙona inna koma ga wannan gudunmawatace ki sai gadon da angonki zai hau ku raya sunnah nayi imani zan samu lada. Kiyi alƙawarin siyan gadon kar ki saɓa Jabu.' Kuɗi masu kaurin gaske ya bani, wanda a wannan lokacin inna canja kuɗin zasu iya kaiwa dubu ɗari biyar irin ta da bata wannan zamanin na tinubu ba. Godiya nayi mishi har tashar mota ni da Uwani muka rakashi dan ita tace zata kwana biyu ta tayani jinyar Dada. Sai da muka ga tashin motarsu yanata ɗaga mun hannu idanunshi fal ruwan hawayen bankwana. Kuka na saka rikitaccen gaske na runtse idanuna tsigar jikina sai tashi take yi. Tausayin Salim ya dirarmun sosai." "Ki dena kuka Iyabo, na fahimci ke kanki bawai son Saleem bane bakya yi ba A'a. Son da kike yima wancan figaggen ne yafi na Saleem. Kamar yadda Hamma yake sonki fiye da Saleem ɗin. Muje magriba ta kawo kai, kiyi haƙuri ki fuskanci yadda zaki fahimtar da gogan naki naga ya ɗauki zafi, fulani dama suna da tsantsar kishi gaskiya. Nifa mamaki iskancin Hamma yake bani " Wallahi Uwani ni tausayi ya bani. Jibi yadda yake kuka kamar ƙaramin yaro fa. Uwani ni nasan raɗaɗin son maso wani. Sannan ni ina gujema matsaltsalun rayuwane. Na tsorata da auren mijin da ba yarenku ɗaya ba. Fulani da yarbawa kuma suna da daɗaɗɗen tarihi na zamantakewa da auratayya. Bugu da ƙari Hamma jininane, ina tsoron kada son abin duniya yasa in zaɓi Saleem harga Allah Hamma nake so" Uwani ta ja gwauron numfashi tace. "Iyabo na fahimta, ni kaina waɗannan tunane tunanenne du banyi su ba. Duk da dai masu iya magana suna cewa abinda aka gasa shi yaji wuta" Fitowa mu ka yi daga tasha muka tari abin hawa zuwa bakin asibiti. Gogan yana tsaye a bakin asibiti da halama ya kafane ya tsare yana son ganin ta inda zan ɓullo. Gabana ya yanke ya faɗi ganin irin kallon tuhumar da Hamma yake yi mun. "Uwani baƙon ya tafi ne?" Ya tambaya yana kakkafe ita uwanin da ido. "Ya tafi Hamma. Dama dai ya matsa ne yana son yaga Jabune, sabida kayan da yawa bazai yiwu ace ya tafi ba tare da ya ganta ba." Murmushi yayi kawai ya kalli tsakiyar idanuna, saiya soma kallon ƙwayar idona da ɗaya da ɗaya. Ta gefena Uwani ta shige. "Wannan soyayyar taku inna tsaya anan Hamma sai zuchiyata ta buga" Cewar Uwani data yi shigewarta ciki. "Me yazo nema a wajenki, kuma me yasaki kukan da har fuskarki da idanunki suka sauya launi?" Wannan tambaya tashi ta sake rikitani, bansan me zance mishi ba. "Ki shiga ciki su Hama da Daso suna ciki. Ni zanje masallaci inna dawo zan raka Hama gida" To Shikenan sai ka dawo" A gurguje na wuce tare da sauke ajjiyar zuchiya a haka dai kamar fishin nashi ya sassauto. A wajen gadon Dada kuma su Daso suna zazzaune a tabarma suna fira ita da Hama ƙawarta. Gefensu kwanukan abincine da suka kawo. Uwani kuma tana zaune a kujerar roba inda nake zama. Ina isowa Hama ta dena hira ta haɗe girarta ta ƙasa data sama. Ita kanta Daso na ga canji sosai a yanayinta. Nasan yana da nasaba da tsaida lokacin aurenmu da Hamma. Sannunku Daso ashe kunzo, ina wuninku?" Daso ce ta amsa babu yabo babu fallasa dai, Hama kuwa bata ce um ba, wasa take da hannun ɗiyarta dake kwance a cinyarta. Uwani wannan itace Daso yarinyar ƙanwar Dada Yafendo Jabu me sunana. Wannan kuma Hama ce matar Yaya Hamma " "Ayya, ai mun gaisa kice itace uwargidanki. Hama Allah ya sanya alkairi Allah ya haɗe kawunanku" "A gaskiya baiwar Allah baki kyauta ba ai ba'ayin haka. Sanin kanki ne babu macen da take son kishiya, ita kanta Jabun da ita za'aima kishiyar aka mata haka ba zata ji daɗi ba" Daso ce tayi maganar cikin fishi da fishin Hama. Sanin halin ƙawata Tabalbalin yasa nace. Kuyi haƙuri itama bata faɗa da niyya ba" Tsaki Hama tayi, Uwani tace. "Allah sarkin girma inji kishiyar mai Ɗuwayya. Allah ya baku haƙuri ni ba baƙuwar zafi bace. Amman fa ku iya bakunanku in kuma ba haka ba sai dai kuji jini na zuba, ƴan iska ƙauyawan banza duk kun cika waje da ƙarni." Duk wannan abun da akeyi Dada bacci take yi. Fulatanci da Hama ta soma zazzagowane ya farkar da'ita. Nasan dai ba alkhairi Hama take faɗi ba. Ɗiyarta ta goya tana ta huci. "Daso meke faruwa ne?" Dada ta tambaya. "Babu komai Dada" Amsar da Daso ta bata kenan. Ana cikin haka sai ga Hamma ya iso. "To muje ko dare nayi. Dada saina dawo zan kaisu gida" "To dama ka zauna a gida. Jabu da ƙawarta zasu kwana anan. Kaima ka huta. Ka sanar da Baffa Musa, inason ganinshi gobe da sassafe. "Haba Dada. Kona koma gidan ma ni bazan iya bacci ba. Likita ma ya tabbatar mana zuwa gobe ko jibi zai sallamemu mu koma gida. Hama muje" Fuuu Hama ta fice ko sallama batai mana ba, Daso ce kawai taima Dada sallama ni ko da uwar harara ma ta bini. Ni kuma nayi mata murmushi kawai nasan kishin rashin Hamma ke damun Daso, ba taya Hama kishi ba. Tunda data samu dama itace zata zama kishiyar Haman. "Ga abinci kuci Jabu. Baƙon ya tafi ko?" E Dada ya tafi" Matashin kanta ta ɗan ɗaga ta gefe ta zaro kuɗin da Saleem ya bata ta miƙo mun." "Ki riƙe a hannunki, ni bansan ma nawa bane. Jabu su Yusufu har yanzu basu zo sun dubani ba" Murmushi nayi mata nasa hannu na amshi kuɗin Dada nice na hanasu zuwa, kiyi haƙuri an kusa sallamarmu mu koma gida" Maimakon naga tayi farin ciki. Sai naga saɓanin hakan damuwa ta bayyana a fuskarta. Babu shiri na ƙarasa wajen gadon na zauna a gefe guda. Dadana na siya miki gidan da zaki zauna ki huta ki mori haihuwa kema. Kuma in sha Allah zan zuba miki kayan alatu da zaki more tsufanki. Kulawarki ta dawo hannuna Dada. Su Cubu zasu zauna tare dake, na ɗauke miki nauyin komai Dada. Nasan ƙila tunanin inda zaki zauna kike yi" Hawayene ya gangaro ta gefen kuncinta, sai ta runtse idanunta tace. Ubangiji Allah ya kai haske kabarinka Akintoye. Haƙiƙa kabar baya me kyau. Jabu kamar yadda sanadiyyarki matsalolin rayuwata suka gutsire. Ina roƙa miki Allah Hamma ya zama silar goge miki damuwar rayuwarki. Sannan inaso in faɗa miki kibi Hama a sannu, sannan kibi Daso a sannu. Ɗazu ba bacci nake yi ba duk abinda suka tattauna duk a kunnena. Dansu a kuɗirinsu shine aurenma bazai yiwu ba. Bokaye sosai Hama take bi duk dan a raba soyayyarku. Ke kuma saiki dage da roƙon Allah yai miki tsari da sharrinsu. Nayi imani da Jabu uwar Daso zata san abinnan da Daso tayi zata iya yi mata baki. Dan haka kija bakinki kiyi shiru komai ma yazo ƙarshe daga gobe za'a yita ta ƙare" Hannun Dada na damƙe na lumshe idanuna. Na lura a wannan tafiyar kamar da jarabawar kishiya kuma zan jarabtu na tsallake rijiya da baya akan uwar miji, ga kishiya kuma jama'a tana neman rayuwata. Babu komai Dada, Allah shi ke da iko akan komai. Ki tayani da adda'a nima zan zage damtse. Ki kuma dena kuka Dada, Allah ya jiƙan Baami" Dawowa nayi kusa da Uwani a tabarma. Na zuba ma Dada jallof ɗin shinkafa dasu Daso suka kawo, har zan miƙa mata sai naga kamar yayi kaɗan sai na saƙa cokali zan ƙara mata. Wallahi saiga dunƙulen magani a cure a waje ɗaya bai idasa cakuɗuwaba. Subhanallaah Uwani duba" Na nuna ma Uwani. Haɓa ta kama tare da zaro idanu. "Iyabo wannan ai dunƙulen maganine, hala kishiyarkice ta kawo abincin?" Da kai na amsa mata. Juye abincin nayi na rufe, na jawo kular Karima matar Amaduyal na zuba ma Dada abincin ciki. Shinkafa da miya da kifine. Na miƙa mata na bata ruwa. Na saka mana cokula biyu a cikin kular zamuci dan sabida ƙauyanci a kan shinkafar ta kyaɓo miyar. "Iyabo jikina yayi sanyi tsoron Allah kuma ya kamani. Tofa wata sabuwa inji ɗan caca. Shi kuma wannan auren na lura da kishiya za'a fafata. Nifa duk harkar asiri bana ciki. Ko kishinne nafi son muyi na kirsa duk wacce ta biya allonta saita wanke. Amman tun kafin ki shigo ciki an soma binki da bita da ƙulli?" Ni dai ko magana wannan na kasa yi. Sai cin abincin nake yi. Abincinma sharkab da mai dan masifa sai tea na haɗa mana muke danne man dashi. Wajajen bayan isha Yaya Hamma ya dawo. Leda ya miƙo mun ɗaya cike da tsire, ɗayar kuma lemun kwalba ne montin dew. Dada ta ɗan jima da bacci sabida magungunanta kamar akwai masu saka bacci. "Ni kam me ya haɗaku da Hama da Daso Jabu" Kallonshi nayi, sai na fahimci ranshi a ɗan ɓaceyake sai nace. Babu komai wani abun suka ce maka anyi?" "E Hama tace mun wai kince kinfi ƙarfin kiyi kishi da'ita dakin shigo zaki kaɗata. Maganganu dai marasa daɗi Daso tace har mahaifiyar Hama kika zage tas. Dan Allah meye gaskiyar wannan lamarin?" Kallon kallone ya shiga wanzuwa tsakanina da Uwani. Tab wata sabuwa inji ɗan caca, ni Iyabo gidan da zan faɗa kuma kenan? Ga asiri ga makirci anya kuwa? Uwani ce naji tayi mishi bayanin abinda ya faru. Sai yayi dariya kawai yace. "Kishi ne yake damunta sosai shi yasa ita da Dason suka ƙirƙiri wannan maganar. Amman zan ɗauki mataki akan ita Haman ni na isa da gidana. Jabu ina jiranki a waje domin ki bani amsar tambayoyina" Yana idasa maganarshi ya fice hannunshi riƙe da sandar da ba'a fiye raba bafulatani da'ita musamman ma masu fita kiwo. Idanuna na lumshe kaina sarawa yake yi sosai. Uwani ci namannan bari inje in kashe wutar da kika kunnamun. Inna dawo zamu tattauna matsaloli Uwani" Nan na bar Uwani tana cusa tsire da albass a bakinta. A inda yake kwanciya na sameshi kanshi a ƙasa yana bubbuga sandarshi a ƙasa. Harna zauna bai ɗagoba, ko salllamata yaƙi amsawa lallai ran maza ya ɓaci. Angona masoyina wanda ya zama zaɓina abun begena. Lafiya ka kasa amsa sallamata, ko dai maganganun da Hama tace na faɗa mata ne suke damunka?" Shirune ya biyo baya na daƙiƙu kana ya ɗago idanunshi ya saukesu a kaina. Na kasa karanta haƙiƙatan ɗin abinda ke cikin idanun nashi, na hango kishi, da so mai wuyar fassarawa. Ajjiyar zuchiya na sauke tare da yin ƙasa da idanuna, ina jiyo yadda idanunshi ke yawo a fuskata. "Wallahi Allah ina da mugun kishi akan duk abinda nake so. Wannan dalilin yasa na kusan kashe ɗan uwan Hama a filin shaɗi a lokacin da ya zama daga cikin gwarazan da suka fito neman aurenta. Jabu kafin ki tafi saida na damƙa miki amanar rayuwata nasa kikai mun alƙawarin babu wani ɗa namiji da zaki bashi damar shiga rayuwarki. Kaico ashe ke soyayya kiketa ta yi. Ni kin barni da dakon sanki, kewarki duk ta hanani sukuni, hatta bacci me kyau ina samune duk ranar da nayi mafarkin na aureki jibi yadda na fita hayyacina Matata da abokaina kullum a cikin surutun lalacewata suke. Amman ke ashe mu biyu kika ajjiye a gurbin zuchiyarki, kin ban mamaki sosai Jabu. Meye matsayin Saleem a wajenki, kuma me yazo yi wajenki, Allah yasa ba kukan sonshi kika yi ba?" Shiru nayi kamar ruwa ya cinyeni tunda ya soma maganarshi harya dure. Akwai taushi da zafi cakuɗe da muryar tashi. Yaya Hamma ka yarda dani kai ɗaya tal ne a zuchiyata ban haɗa soyayyarka data kowa ba. Ko uban Ƴaƴana ban soshi irin son da nake yi maka ba. Gaskiya dai ɗaya ce Saleem ya taimakemu a zamanmu na saudiyya. Dan shi yai mana hanya muka dawo Najeriya. Bamu yi soyayya ba, amman ya soni sosai. Dalilin zuwanshi kuma neman aurena yazo yi, kuma na faɗa mishi gaskiyar lamari. Batun kuka kuma ka gafarceni tausayi ya bani ne" Ƙur idanunshi a kaina yana kallona irin kallo mai fassarar ban yarda dake ba. Idanu na lumshe na buɗe a kanshi. Yaya Hamma" Yayi saurin ɗaga mun hannunshi. Yayi magana da wata murya a ciki. "Ya'isa haka dan Allah. Kar kiyi sanadiyyata inje in rataya a wuyanki. Ki koma ciki (🤣🤣) Uwani na jiranki saida safe" Nayi yinƙurin fahimtar dashi tare da rarrashinshi. Amman bai bani wannan damar ba sam. Haka na miƙe jiki da zuchiya babu kuzari na shiga na samu Uwani tana waya. Jagwab na zauna a gefenta ina ambaton Allah. "Lafiya na ganki haka Jabu, an samu tsabanin fahimta da Hamma kenan ko?" Ke dai bari yaƙi fahimtata akan zuwan Saleem Uwani. Amman zan bashi lokaci inya huce zai fahimceni. Ni wallahi komai ya fice mun arai, Hama lamarinta ya kashe mun jiki. Tsorona Allah tsorona hulɗa da mai mu'amala da bokaye Uwani. Wannan wanne irin zama zamuyi kenan, da wanne irin bita da ƙullin zata bini in mijin ya zama namu mu mu biyu?" Uwani ta muskuta kana tace. "Adda'a takobin mumuni, bacci da barin bakinki shiru ba naki bane. Ni a tunanina da ai miki kisan mummuƙe aita gabza miki asirinma baki sani ba. Ai gara kin sani zaki san irin zaman da zaki yi da'ita. Ke dai ki zama me lura sosai. Kar ki sake kici duk abinda zai fito daga hannunta shine kawai tunda kin nace. Abinne Allah cuta Allah magani, tunda ko kai akazo aka tarar bakasan irin wacce za'a kwaso maka ba. In kinga irin yadda amaryar Hafizu take tata ɗiban albarka irin nasu na ƴan ƙauye Iyabo zaki riƙe baki. Kinsan akace shege na ƙauye." Dariyar dole Uwani ta bani, duk da labarin da take bani mai ciwone a gareta itama saida ta dara. Bani labarin yadda ta kaya a tsakaninki da Hafizu ranar da kika koma" "Hahahahhh baki da kyau Iyabo. A daren ranar ni ban barshi ya shigo mun ɗaki ba. Kafin ya dawo na garƙame ɗakina. Bugun duniya banbi ta kanshi ba, sai matarshi ce tazo ta jayeshi tana cewa wai ya barni ƙila bacci nake yi. Sai da safe dana buɗe ɗakina ya shigo muka gaisa sama_sama, ni dai naƙi sakin fuskata sai jana da hira yake yi nayi biris dashi. Ke saiga wani dumamen tuwo da wani ƙazamin ruwan kokko harda dogon gashi a ciki matarshi ta shigo ta dure mun. Ke dai kinsan banda daɗi Iyabo, a taƙaice dai na sai gida a can saman layin ta titi, ɗakuna ukune sai banɗaki da kitchen harda shago a ƙofar gidan, nayi komawata. So nake inna nutsu a gyare mun shagon in soma kasuwanci a ciki, in Allah ya dafa mun shikenan fa Iyabo. In Hafizu yazo miji, in baizo ba shi da banza basu da maraba. Bazan kashe kaina ba wallahi sabida rijalu. Ko yanzu ya tafa mun takaddar sakina cafewa zanyi in cashi zawarci" Kai na jinjina ina dariyar furucinta na kusa da ƙarshe da tace in yazo miji, in baizo ba shi da banza duk ɗaya. Uwani ta balbalin duniya. A irin zafinki kam zama gida ɗaya da kishiya ba naki bane, raba gidan yafi. Koni da ace Hamma zai amince mun da saina sai waje na gina inyi zamana a gidana da saina fi samun nutsuwa. Amman kinsan ƴan ƙauye su gidan gandunnan shi suke yi, kowa dai da ɓarayinshi." "Amman dai zaki gyare ɓangaren naki yadda zaki ji daɗin zaman wajen ko? Ina tausayinki Iyabo baki san sharrin rijalu bane hmm" Murmushi nayi nace. Sai dai in gyara cikin ɗakin nawa, wallahi Uwani bana son inyi wani abun da zai haskoma Hamma kamar na raina arzikinshi. To iyakar gyara zan yishine a cikin ɗakina" Harara ta watso mun taja dogon tsaki ta jiya baya ta kwanta. Uwani meye haka?" Cikin masifa tace. "Da Allah Iyabo mu bar zancannan ni bacci nake ji naga kamar kin zama majuniniyane akan Hamma" Dole haka zancan ya tsaya. Ni kuwa na jima cikin tubka da warwara da ƙyar bacci ya ɗaukeni cike da mafarkai marasa daɗi masu tada hankali. Gabaki ɗaya saina wayi garin cikin damuwa da fargabar data haifarmun da zazzaɓi. Da sassafe saiga Yafendo Kaɓoji, da Baffa Musa sunzo. Dada tace mu basu waje, me suka tauna oho basu jima ba suka kama hanyarsu. Muna komawa ciki saiga takaddar sallama da ragowar kuɗaɗen da ake binmu. Gashi yau tun sassafe Yaya Hamma ya bar asibitin. Uwani ta zauna da Dada ni kuma naje na biya kuɗin da ake binmu. Ina dawowa na tarar da Amaduyal shi da Kari matarshi. Kari ce ta tayani tattare kayayyakinmu tsab, Amaduyal kuma nace ya fita ya nemo mana ƙaramar mota zuwa Girai. Ai kuwa hakan akayi motarnan ta saukemu a Girai muka hau akori kura zuwa Banyo, daga Banyo muka ƙarasa jaɓɓi. A sabon gidan Dada muka sauka. Ta kalli gidan ta kalleni saita saki kukan farin ciki ta dubeni tace. ", Jabu Allah yayi miki albarka. In sha Allah Kamar yadda kika sani zubar da hawayen farin ciki. Rayuwarki zata yi albarka. Allah ya jiƙan Adetoye da rahama." Ameen Dada nagode sosai mu shiga ga ɗakinki nan. Wancan nasu Cubu ne, sai na su Yusufu gashi can." Ɗakin muka shiga daga gado sai wata kujera doguwa guda ɗaya, sai kafet malale a ƙasan ɗakin da labule, sai akwatin kayanta guda ɗaya. Kayan ciki sababbi nasa aka ɗinko mata da hijabinta biyu da takalma biyu sai dadduma. Kan kace me labarin sallamomu ya kareɗe ƙauyen nan mata suka cika gidan ana ma Dada Yaya jiki ana mata barka da arziki. To nima anan nake cewa mu tara gobe in Allah ya kaimu.... MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (2) Ni da uwani kuma muna madafa na hura kara ina kiciniyar ɗaura girki ta dubeni tace. "Iyabo yanzu kema da karar zaki dinga girki in kunyi auren ko? Ni wallahi Iyabo ba wai ƙin Hamma nake yi ba, ba kuma ƙyamatar rayuwarsu nake yi ba. Ke nake jiye ma, kece baki saba da irin wannan rayuwarba, su fes suke jin kansu ba wata matsala, ta ina ke zaki soma Iyabo?" Murmushi nayi mata ko a jikina nace. Nifa babbar nasara shine in zama mallakin Hamma kawai, kuma inason in zauna da Dada, aurenta fa ya mutu faɗa miki ne banyi ba uwani. Uwani zuchiyata tayi nisa da sonshi, idanuna ya rufe bana hango komai. Bini da adda'a ƙawata kawai, ki dena damun kanki. Da birni da ƙauye duk rayuwar ɗayace, ita mace kwanciyar hankali take buƙata a gidan aure ba birni ko ƙauyeba, sannan inason in koya ma ƙannena yadda zasu bautama Allah. Hatta Dada daga iya alwalarta akwai gyara ina ga karatun Sallah kuma." Dariya tayi kafin tayi Magana kawai sai muka jiyo guɗar su Boɗɗo da su Cubu, harda Yafendo Jabu. Kuma wajenmu suke nufowa. Suna shigowa Baɗɗo tace. "Adda yau dai kin zama matar Yaya Hamma an ɗaura aurenku babu jimawa" Farin cikine, a'a ruɗewace sai kawai naji gudawa ta kamani. Kafin in miƙe sai Yafendona tace. "Munyi farin ciki da wannan Aure. Muna fatan mutuwace zata rabaku. Adda Daso sai kukan farin ciki take yi" Ni dai da jin wannan labarin saida nayi gudawa sau biyar cikin awa guda. Ina cikin wannan zuruftu saiga Hamma da abokanshi biyu sun kutso kai gidan. Nayi maza na shige kitchen dan yafi kusa dani. Idanu na lumshe inajin wani farin ciki na cikar buri na lulluɓeni. Amman sun sammaceni, babu shakka wannan shine dalilin zuwansu Baffa Musa da safe asibiti, kuma shine dalilin Dada na cewa za'ayita ta ƙare, ashe tana nufin auren za'a ɗaura kowa ya huta. Uwani ce ta dafani nayi saurin buɗe idanuna. Sun tafine uwani?" Na tambayeta ina dariya. Itama dariyar take yi tace dani. "Sun tafi, dake da Hamma bansan wanda yafi wani farin ciki ba. Bakiga bakinshi ba yaƙi rufuwa sam. Ina miki fatan alkhairi Allah yasa ki samu farin ciki ɗorarre na zubar da makaman yaƙina iyabo, Allah ya ƙadarto miki rayuwa a rugga" Ameen Uwani ko ke fa. Yanzu dai me ake ciki dangane da kayan ɗaki? Ni a kano naso sayen gado da kayan kujeruna gaskiya, to yanzu ba lallai lokaci ya bamu damar hakan ba" Baɗɗo ce ta shigo tace. "Adda kizo Baffa na son magana dake" Uwani ki dinga duba girkinnan kafin inzo' Nasa kai na shiga ɗakin Dada da sallama. Dukka ƴan uwan Dada suna ciki. Yafendo Kaɓoji tace. "Tawo ki zauna a kusa dani ƴata" Cike da kunya na ƙarasa na zauna a gefen ƙafarta. Baffa yace dani. "Ungo nan Jabu sadakinkine nera dubu biyar. Ɗazu aka ɗaura aurenki a ƙofar gidan mai gari ke da Hamma. Amman kasancewar auren yazo babu wani shiri, inda zai saki ma bai gina ba tukunna zaki zauna a gida kamar na sati biyu kafinnan ya gama ginin ya kuma gama haɗa lefe sai ki tare" Hannu nasa na amshi sadakin. Na kuma ji daɗi sosai da akace mun sai nanda sati biyu zan tare. Har zan shiga Kano inje inyi gyaran jiki in kuma siyi kayan ɗaki irin wanda raina yake so" Yafendo Kaɓoji tace. "A'a Yaya sati biyu yayi yawa. Ginin yau zasu soma da abokanshi zasu iya gamawa yau. A bar dai tariyar rana ita yau zaifi" Dada tace. "Allah ya nuna mana rana ita yau ɗin. Amman ita Jabu gobe zata koma kano kamar yadda na sanar daku, acan za'aje a ɗakko Amarya a wajen dangin mahaifinta suna da hakki. Da ace lafiya nake da ni da kaina zan kaita inyi ma Toyosi ɗin bayani a nitse dan gudun kar suga kamar anyi musu fin ƙarfine." Baffa Musa yace. "Hakanma yayi, babu damuwa ku zaku tsara yadda tafiya ɗakko Amaryar zai kaya. Allah ya sanya alkhairi. Jabu zaki iya tafiya sai ki kwana da shirin tafiya kanon gobe. Duk abinda zaki kintsa saiki kintsa rana itayau za'a zo ɗaukar taki, ki sanar musu suma acan. To Baffa " Iyakar abinda na iya cewa kenan. Na fita na samu Uwani na labarta mata duk yadda mukayi. Haka dai muka wuni tarbar baƙi masu zuwa dubiya. Su Yusufu duk suna gidan sun shige ɗakinsu da abokansu. Sai da daddare Hamma ya samu zuwa muna tsakar gida mun gama cin abinci munyi sallar isha anata hira ina jin daɗin kasancewata tare da ƙannena, sai gashi ya shigo da sallamarshi. "Ango kasha ƙamshi lale da zuwa" Cewar Uwani kenan tana tsokanarshi. Hannunshi riƙe da ledoji biyu. Sai ya miƙa ma Cubu leda ɗaya yace ta kaima Dada. Ɗayar kuma yace ta Uwani ce, na karɓa na miƙa mata. Watsewa sukayi suka barmu mu mu biyu a tsakar gidan. Ni ina kan tabarma shi kuma yana kan jarkar ruwa yana fuskantata. Ina wuni Yaya Hamma? Na faɗa a sanyaye da sabuwar muryar da baisan na mallaketaba. Wata iriyar muryace mai kama da busar sarewa." Sai da ya sauke ajjiyar zuchiya nannauya kana ya dubeni muka haɗa idanu sai yace. "Faɗa ya ƙare Hamma yayi nasarar samun Jabu na kayar da mutan birni." Dariya ya bani sosai. Yaya Hamma kenan. To Allah ya bamu zaman lafiya. Allah ya baka ikon yi mana adalci a tsakaninmu" "Ameen nagode da wannan adda'ar taki. Sai batun tarewa Dada tace an tsayar da maganar tarewa sati me zuwa. Kuma a Kano za'aje a dakkoki ko?" Kai na gyaɗa mishi. Sai yace. "Maganar kayan lefe zan baki kuɗinne ki siyo abinda kikeso a Kano harda fantimoti ko yaya kike ganin za'ayi?" Duk yadda kayi daidaine na baka wuƙa da nama" Kai ya girgiza yace. "Ni kinga bansan kalaba. Sannan Hama ma ba sanin kala tayi ba bare in bata ta haɗo komai" To ka tuntuɓi su Dada ko su zasu haɗa ni basai na haɗa lefe ba" "To Shikenan Amarya yadda kikace haka za'ayi. Zan tuntuɓi matar ogana na birni naga kamar kayayyaki take siyarwa in yaso sai in bata ta haɗamun duk abinda ya dace. Yanzu nawa kike buƙata na gyare_gyarenku na Amaren birni?" Dariya nayi mishi. Shima dariyar yayi. To kuɗin gyaran jiki, sai kuɗin ƙunshi, da kuɗin kayan fitar biki Shikenan abinda nake buƙata" Hannu yasa a ajjihu ya zaro nera dubu goma sha biyar Murtala _murtala ya miƙo mun, nasa hannu na karɓa nasa musu albarka." "Gobe zanzo in kai ku tasha, dama inason zan sai fenti a birni mun gama gina miki ɗakinki. Duk da dai ban samu yadda nake so ba lamarin yazo mun babu shiri" Zamu rabu kamar ba zamu rabu ba a wannan dare mai cike da ni'ima iska sai kaɗawa take yi hadari na rugugi a sararin samaniya. Ganin an soma yayyafi yif_yif yasa ba dan rai ya so ba muka rabu da juna cike da shauƙin junanmu. Washe gari sassafe muka shirya tsab Yaya Hamma yazo ya kaimu tasha har sai da motarmu ta bar tasha suka tafi shi da aminanshi. Bayan la'asar sakaliya muka shiga gida. Su Iya duk suna tsakar gida suna murnar haihuwar Bose muka tarar dasu. Nan murna ta zama bibbiyu. Sai da muka nutsa muka rama sallolin da aka boyomu, Uwani tai ma Iyaa bayanin duk abinda ke a kwai. Da jin wannan bayani sai Iyaa ta miƙe tsaye tana buga cinyoyinta tana faɗin. "Mo ti pari mo ti pari ah ah ahh.. ( na gama yawo, na gama yawo) Iyabo aure a ƙauye a wannan garin zaki zauna kiyi zaman aure? Kin kashe rayuwarki, kin kashe kanki" Kafin kwabo Sai gasu Iyaa Beji da su Iyaa Kokodeen sun shigo. Bata sauya zane ba. Ita dasu duk kanwar ja ce, sukaita kwakwazo har sai da Alfa ya shigo shine ya tsawatar musu. Iyaa kuwa du hannuwanta aka ta ɗorasu tana jijjiga harda hawaye shaɓe_shaɓe tana ta ambaton Ah ah ah...." Wanda indai kaji beyerabiya nata maimaita wannan kalma to fa abu yayi abu. Alfa ya tambayi Iyaa Kokodeen meke faruwa. Kafin tayi magana Iyaa Debisi ta soma magana da yare ta bashi labarin abinda Uwani tace mata. Jimm yayi sai halamun tsoro suka bayyana a fuskarshi muraratan. "Je otito Iyabo?" ( Da gaske ne Iyabo) Ya tambayeni idanunshi kakkafe a kaina. Beeni ( Eh)" Itace kalmar dana furta a sanyaye. Shima jikinshine ya kuma mutuwa mus. Gwauron numfashi ya sauke yace. "To Allah ya sanya alkhairi. Tunda rayuwar da kika zaɓama kanki kenan mu bamu da abinda zamu ce dake. Toyosi kiyi haƙuri ki bita da adda'a a wannan karon kar ku juya mata baya." Da ƙyar ya rarrashi Iyaa ta haƙura. Ni da Uwani dai duk mun takure, Uwani taso tafiya ma, amman ganin irin faɗan da Iyaa ta dinga yi mun yasa dole muka kwana tare. Washe gari ragowar samari da magidanta gidanmu duk labarin aurena ya ruskesu. Kowa sai jimantamun yake yi. Burodami Debisi kuwa kamar zai yi hauka da yazo gidan yaji labarin abinda ake ciki. Ƙasa zaman gidan yayi ya fice. Nan Iyaa ta sake saka ɗambar faɗa tana faɗin. "Ai duk Debisi ne ya ja wannan abun. Tunda tun farko dashi ya auri yarinyarnan da sai dai mutuwace zata rabasu. Gashi yanzu ta kashe rayuwarta a banza, wawuyar yarinya wadda batasan meke mata ciwo ba. Ko da yake Daso ce ta zuga ta shi yasa ta jayeta su je su sha wahalar tare" Iyaa ta dinga jero zance babu arziki muka shirya tsab muka bar gidan. Da gidan Bose muka soma, sai muka nufi gidan Uwani data siya. Hafizu yana zaune a kan benci a ƙofar gidan sai gamu. "A'ah Alaja Iyabo rakiyarce kuma har Kano? Lallai wannan ƙawance naku da girma yake" Ya ƙarashe yana dariya sai kace wanda yaga wawan zama. Uwani kuwa girar sama ta haɗe data ƙasa, ta buɗe gidanta tayi shigewarta ta barmu muna gaisawa dashi. A tsakar gida na sameta tana kiciniyar buɗe ƙofar ɗaki. "Taho ki soma ganin dilolin kayan. Da mun gama hidimar biki zan buɗe dila amman nafi son in gyare shagona tsab." Ta buɗe ɗakin muka shiga, ga dilolinan masha Allah, wani kan wani dukiya akwai daɗi ganin dilolinnan sai ya sharemun ƙuncin da su Iyaa suka dasamun a raina. Ɗakin uwani muka koma, ɗaki masha Allah har kayan kallo Uwani ta saka ga firjinta ƙatoto. Kinyi gyara gaskiya Uwani. Kuma gidan yayi kyau babu laifi" "Wallahi kinga ga wani gida na jikin nawannan daga hannun hagu, shima da shago babbane dan yafi nawannan girma. Ni dai da zaki siya ko haya sai ki zuba Iyabo, ki ɗan dinga karɓar kuɗinki, kuma ko babu komai kin ajjiye kadara. Gidan a hannun dillalin dana siya wannan gidan ta hanyarshi yake. Yana ta mun tayi gidanma akan in siya in haɗe da nawa. Ni dai ki siya Iyabo. Ina da kuɗin siya amman ke naima sha'awar gidan " To Uwani naji shawararki zan siya babu matsala, dan dama shanu naso in siya ayimun kiwo. Ammam bazai gagaraba zan sai gidan" Uwani bata ƙyaleni ba har saida ta kaini ofishin dillalinta muka tsayar da magana harda rabin kuɗi na ajjiye mishi mun tsaya akan gobe inzo da shaiduna insa hannu a takadda a mayar da sunan gida nawa a bani takadduna, in cika kuɗi a bani ɗan makulli. Hakan kuwa akayi Burodami Kokodeen da Lekan sai Uwani su su kaimun shaida akayi aka gama komai aka bani takaddun gidana da ɗan makulli. Ɗakuna shida ne falle falle, sai ban ɗaki da kitchen, da shago a waje kamar dai gidan Uwani. Daga haka muka shiga sha'anin gyaran jiki, magungunan mata daga wajen Anty Ramlex, shiga kasuwa, kai dinki. Kafin dai sati guda duk abinda zan siya na siya na jibge a gida har dilolin kayana nasa mota ta ɗaukarmun ta kaimun gida. Na buɗe jakar tsaraba naba duk wanda ya dace. Ranar laraba sai ga mutanen Banyo da yamma sakaliya mota ɗaya duk mata, sai direba namiji. Sun samu tarba ta girmamawa sosai dan ni banyi tunanin hakanba ma. Sun tawo harda akwatinsu mai taya guda biyu. Kayan ciki babu yabo babu fallasa ga bazawara kamata dai. Wasu a ɗakin Iyaa Debisi suka kwana, wasu kuma a ɗakin Iyaa Kokodeen suka kwana. Ni da Uwani muka kwanta a ɗakin su Lekan. Washe gari sassafe muka ɗauki hanya. Motar da suka tawo da'ita ɗaukar Amarya muka shiga mu biyar. Ni da Uwani, sai Anty Ramata, da Iyaa Kokodeen. A gaban mota kuma Burodami Kokodeen ne sai direba. Motar kaya kuma aka lode kayayyakina hardasu dilar kayana aka rufe da tampol dan hadarine baƙi ƙirin a garin motar kayan ta daɗe da kama hanya ita kafin mu. Muka kama hanyar Adamawa. Tun kafin mu fita daga cikin garin Kano aka soma yayyafi sama_sama. Da muka soma shaga ƙauyuka ruwan yanata ƙaruwa, duk ƙauyan da aka wuce ruwa akeyi sosai. Sai tafiyar ta zama me daɗi babu zafin rana sam sai sanyi dake ratsawo ta ƙasan motar. Su Iyaa Kokodeen tuni sukai baccinsu sai gwara kai suke yi. Idanu na lumshe inata tunani, tare da adda'ar Allah yasa kada Yaya Hamma ya bani kunya ya tozarta zumuncinmu. Yanzu Shikenan rayuwata ta koma ƙauye nima zan zama baƙauya kenan? Wasu siraran hawayene suka gangaro a kumatuna wanda ni kaina bansan na meye ba. Haka mukaita gudu har muka isa Adamawa ruwa akeyi sai tsurarun ƙauyuka da basu wuce uku ba da muka wucesu ba'a ruwa. A Girai motocinnan suka tsaya gashi ruwa akeyi sosai. Haka dole muka fita daga cikin motar muka fake a ƙasan wata bishiya mai yalwar ganye. Maza da mata duk muna fake mota ake jira. Munfi awa guda ana zabga ruwa daga bisani ruwan ya tsagaita mota ta tawo duk ta kwashemu. Kowa a takure yake sanyi ga jikewa da mukayi amman ba sosai ba. Hanyar tafi ta kullum muni, ko ina ruwa camɓal a kwance, ga laka sai riƙe motar take yi a haka dai har muka iso masauki. Daga nan muka tari mashina suka shigar damu. Gidan Dada kai tsaye nace su wuce dani dan ina buƙatar in sake kayan jikina, ba a kai amarya a jike sharab ba. Dada da Yusufu ne kaɗai a gidan tana ganin su Iyaa Kokodeen ta soma murna tana musu yare. "Daso ciwo kikayi haka naga duk kin ƙare sai wuya?" Dada ta dubi Iyaa Kokodeen tace. "Zauna tukunna manyan baƙi nayi farin ciki da ganinki. Yau gaku a garinmu." Zazzaunawa sukayi Jikkunansu duk a mace. Sai jimantamun suke yi. "Ni ina mamakin abinda Iyabo ta gani da har ta amince da rayuwar ƙungurmin ƙauyen nan. Rayuwar ƙauye a wajen ɗan birni takota ina cutarwace. Jibi nisa da wuyar da muka shawo. Ohh ke kuma haka kikeson kaddararki ta kasance" Cewar Iyaa Beji kenan. Iyaa Kokodeen ita kam hawaye take ta sharewa. Take nima na fashe da nawa kukan sai shessheƙa nake yi. Ni wannan maganganun duk sun isheni. Ni ba yarinya ƙarama ba, kuma ni nace naji na gani ba sai su sa albarka su bini da ido ba? Haka aurena da Gwadabe akaita koke_koke da tashin hankula iri daban_daban gashi a aure na biyu dana auri jinina bata sauya zani ba. Ko babu komai ni inaso in zauna a kusa da kannena da mahaifiyata. Tunda da tun farko an barni a hannunta da a wannan ƙauyen zan rayu, kamar yadda itama ta rayu." Kaya na sauya, akwatin kayan sawata dama yana tare damu. Ruwa daya tsagaita Yusufu yai mana jagora bayan mun rama sallolin da ake binmu har magriba munyi, an kawo mana jallof ɗin shinkafa da Dada tasa aka dafa domin tarar baƙi. Yafendona Dada ta aika aka kira duk suka haɗu aka rankaya kai Amarya da ƙafa. A kacame gidan yake sosai anata kacaniyar biki. Tsakar gidannan ta damalmale da ruwa da abinci da yara suka zubar. Rumfunan gidan cike da mata da yara anata haya_haya. Ɗakin Yafendo Kaɓoji aka wuce dani kai tsaye. Anan muka tarar da su Yafendo A'i da yaransu mata dake gidan aure. "Lale lale. Amaryarmu tazo gida. Sannunku mutanen Kano" Waje aka basu na zama aka taresu da lafiyayyen tuwo miyar ta wadatu da naman saniya da man shanu. Yafendo A'i tace. "Ga abinci kuci, ayi sallah sai a shiga da Amarya ɗakunan matan gidan kafin a shiga da'ita ɗakinta. An gama jera mata komai. Tun ɗazu mata suke zuwa kallon ɗakin Amarya tubarkalla masha Allah" Ɗan dariya Iyaa Kokodeen tayi a matsayin amsa kawai. A nan mu kai Sallah, Baɗɗo ta shigo ta sameni. "Adda ragowar wasu muhimman kayanki duk suna ɗakina gudun kar a ɓarnatar miki. Akwai ƙunshi wasu buhunhuna duk na shiga dasu ɗakina" Yauwa Baɗɗo su waɗannan buhunhunan ki barsu a ɗakinki zuwa gobe zamu ware kayan amfanina ragowar gidan Dada za'a Kai mun." Raɗa naima uwani a kunnenta, ta miƙe suka fita ita da Baɗɗo. Yafendona tace. "Iyayen Jabu ku taso mu kai amarya ɗakunan matan da tazo ta tarar a gidan bisa ga al'ada kafin a kaita ɗakinta" Gaba suka tusani Yafendona da Iyaa Kokodeen. Ragowar kuma aka nuna musu ɗakina suka kama hanya. Da ɗakin Hama muka soma, ɗakin ma cike yake da ƙawaye babu masaka tsinke. Duk sun tarune domin suna son ganina, ance musu daga Saudiyya na dawo. Sai da wasu dole suka fita kafin mu muka samu waje. Yafendona ta nuna mun gefen gadon Hama tace. "Jabu ga bakin gado zauna muyi a gurguje ki samu ki shiga ɗakinki sanyin yayi yawa" Ɗofanuwa nayi a bakin gadon, fuskata ba'a rufe take ruf ba ina iya ganin kowa da komai, duk wanda ya kalleni zai iya ganin fuskanta. Hama fuskarta ta kumbura tayi jawur da halama taci kuka ta gode Allah. Dan ina zama ta bani baya sai jijjiga ƙafarta take yi. Ga Daso a gefenta sauran manyan ƙawayen nata suna tsakiyar gadon sai ƙaremun kallo suke yi. Ni ko ina lure tsab da motsin kowa. "Hama ga ƙanwarki mun kawo miki. Duk da dai zata iya girme miki amman dole kece sama da'ita tunda ke ta shigo ta samu. To Jabu dai ba baƙuwa bace ku daure ku haɗe kawunanku domin a zauna lafiya. Jabu dai ƴar uwa take ga Hamma da mahaifiyarta da mahaifiyar shi uwa ɗaya suke uba ɗaya kin sani. To ayi haƙuri a martaba wannan halaƙar" Hama dai taƙi buɗe bakinta tayi magana har saida Daso ta zungureta kana tace. "Allah ya bada zaman lafiya ya sanya alkairi " Yafendona tace. "Ameen to Jabu muje a kaiki ragowar ɗakunan" Haka mukaita shiga ɗakunan matan ƙannen Hamma daga ƙarshe suka wuce dani bukkata dake wata ƴar kwana can ƙarshen gidan sai an shiga lungu. Tun daga ƙofar lungun akayi blue ɗin fenti har cikin bukkarnan data kasance ɗakina. Da bismillah na shiga ina karanto adda'a duk wacce tazo bakina. A takure bukkar take sosai kasancewar kayana da yawa sai ya zamana babu ko wajen da zan iya sallama. A kujera aka zaunar dani. Uwani da Baɗɗo sai gyare_gyare suke yi mini. Anti Ramata tace. "Allah me iko. Yau wannan shine ɗakin auren Iyabo" Sabida rashin waje ishasshe basu jima ba duk suka fice, ɗaki ya rage daga ni sai su Uwani. "Iyabo kujerunnan dole ki rabu da wasu gaskiya. Ni ina ganin waccan 2 sitter ɗin kawai za'a bari in kinaso ki samu fili. Sannan kayayyakin kitchen ɗinki fa duk mun lode miki a sib ɓangare ɗaya baki da kitchen, da kitchen da banɗaki duk na gandune, kinga ai ba zamu yi miki jere a kitchen ɗin gandu ba. To Uwani duk yadda ya dace ayi kawai" Nace da'ita ina takure a kujera" "To yanzu dare yayi zuwa gobe da safe duk saimu gyara komai ni da Baɗɗo. Kun haɗu da angon naki kuwa Iyabo?" Idanu na lumshe nace. A'a bamu haɗu ba, ƙila ma sai gobe dare yayi, gida kuma haɗe da iyaye" Mayafina na cire na koma kan gadona da yasha lafiyayyen zanin gado mai laushi. Fentin ɗakin nabi da idanu, bai biyu ba yayi wani roɗi_roɗi. Na ɗaga kaina azara tana kallona ina kallonta. Ajjiyar zuchiya na sauke na dubi Uwani nace. Uwani wannan azarar babu yadda za'ayi a rufeta?" Dariya ce ta kama Uwani sai da tayi mai isarta sannan tace. "Zamu rufeta zuwa gobe ko da zanin gadone, dan dama nace zan shiga gari in siyo cottin a zagaye miki ɗakin dashi zaifi fasali fiye da wannan fentin ƴan ƙauyen a hakanma naga ke kaɗaice mai fenti me kala duk farar ƙasace a shafe a nasu bukkar, azara ai ke kika siya da kuɗinki Iyabo. Ke dai zuwa goben dai ki kwantar hankalinki Amarya a gidan Hamma." Dariya muka saka dukkanmu nace. Baki da dama Uwani Uwargida a gidan Hafizu, Hafizu ikon Allah" Wata uwar harara ta watso mun. Na sake fashewa da dariya. Baɗɗo tace. "Bari in kawo muku fura da nono Adda" Ta fita sai gata da Fura da nono cikin ƙwarya, tayi mana sallama ta fita dan a lokacin goman dare zai iya yi. Muna daga gado muna hira da Uwani muna shan fura. "Iyabo nifa harna hango miki alkhairan kasuwanci. Wallahi in Allah ya dafa miki me kuɗi zaki zama, kita sare_sarenki. Nima kafin in tafi zan sari man shanu. A hannun Baɗɗo tunda yanzu lokacin arharshi ne." Mun daɗe sosai muna tattaunawa kafin bacci yayi awon gaba damu. Washe gari aka kuma tashi da hatsaniyar biki. Uwani tun wurwuri suka shiga gari ita da Baɗɗo. Daga ni sai Anti Ramata a ɗakin, sai wajajen takwas na safe matar ƙanin Hamma ta kawo mana shayi ruwan bunu da ƙaton biredi sai ƙosai cikin kula. Ni banci biredin ba ma, ƙosai biyu naci sai ruwan bunun dana sha. Cubu ce ta leƙo ɗakin tace. "Adda na kai miki ruwan wanka ki je ki watsa" Dama tuntuni wankan nake son yi inje mu gaisa da Yafendo, da ragowar matan gidan. Hijabi na saka na fita hannuna riƙe da kwandon soso da sabulu. Ruwan wankan yana cikin sabon bokitin ƙarfe in leƙa ruwan sai naga wani garin magani yana yawo a cikin ruwan. Baki na buɗe ina mamaki, ba shiri na kelayar da ruwan na fito da bokitin a hannuna. Da hannu na yafito Cubu dake gindin murhu. Tana ƙarasowa na damƙa mata bokitin. Ungo ki zubo mun wani ruwan zafin. Kafin ki zubo ki ɗaurayo bokitin sosai. Wancan zamewa nayi ya zube" Karɓa tayi ta zubo mun wàni ruwan nayo wanka zuchiya cike tab da fargaba. Ina fitowa na kintsa cikin riga da siket na atampa, na yi kwalliya sama sama na yafa mayafina wanda na bishi da turaren feshi. Ina fitowa tsakar gidan ido ai sai ya dawo kaina. Anan zan dakata sai Allah ya kainmu gobe. MRS BUKHARI Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 *Ƴar uwa ina fatan baki mance da kayan ƙamshin Mrs Bukhari gidan ƙamshi ba ko? Ƴar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ƙamshi. Matso kusa ƴar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ƙamshi ya riƙe miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake saƙawa a tsakankanin kaya. Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ƙamshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata. Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haɗe da turaren fesawa a gashi. Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ƙara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ƙamshin kifi ɗanye. Inada humrori kala_kala. Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ƙamshi. Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ƙamshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ƴar mutan Maiduguri kin samu ƙamshi. ( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai ɗauke da abubuwa huɗu manya kuma a kan kuɗi ƙalilan karki bari garaɓasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)* 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (3) *Yau juma'a karku manta ranar lahadi kayan promo zasu tawo arewa.* *Waɗanda basu turo kuɗinsu ba su turo dan Allah* Kunsan masu ƙiba yadda sutura take amsarmu, haka kwaliyarma take amsarmu. Abunka kuma da Amaryar birni a ƙauye. Ni dai harna iso gun_gun matan dake kallona basu dena ba. Ina kwananku" Nai musu jam'u dan Hama ma tana cikinsu. Tsirari daga cikine suka amsa, na yi wucewata na bar musu ƙamshin turarena a iska. Danƙari na ji wata baƙuwar murya ta faɗa ko me take nufi da hakan oho. Sallama nayi a ƙofar ɗakin Yafendo na shiga. Duk ƙannen Dada suna ciki karyawa suma suke yi, su Iyaa Kokodeen ma suna ciki. A ƙasa na zube na bisu ɗaya bayan ɗaya na gaishesu. Ko wacce da fara'a ta amsani. Saina nemi gefen gadon bono na takure kaina a ƙasa nayi shiru kamar ruwa ya cinyeni. Can Yafendo A'i tace. "Jabu sai kin ƙara da haƙuri dan zama da kishiya ba abu bane mai sauƙi ba. Musamman ka haɗa miji da bafulatana, bafulatanar ma ta Camaron basu ɗauki kishi da wasa ba. Mu ma da kika ga mun yi ƙarko har zuwa yanzu, haƙuri da kawaicine, da ƙarfin adda'a. Kema ina baki shawarar ki riƙe wannan abubbuwan zaki samu riba duk daren daɗewa. Ki zamto mai kawo haɗewar kai ba mai ƙoƙarin ganin an samu rabewar kai ba. Hamma dai ɗan uwankine jini ba ruwa bane, kar ki bari wata ta kutso kanta cikin rayuwar aurenki ki kula sosai. Kuma kin nuna mana soyayya, kin yi abun a duba Hamma zai nuna miki shi ɗan halak ne" Ta jima tana nusar dani tare da bani satar amsa dangane da yadda zafin kishin fulani yake mazansu dama matan nasu. Daga ƙarshe tace inyi komawata ɗakina" Sallama nayi musu na fito. Kaina a ƙasa na wuce matan da suke tsaye cirko_cirko dan son sake ganina. Uhm bance dasu ba nayi kwanar lungun ɗakina nayi shigewata. Uwani na gani akan turmi tana ta faman zagaye mun ɗaki da farin citton me les les. Yayi matuƙar kyau sosai. Ashe kun dawo Tabalbalin? Sannunku da ƙoƙari" "Mun dawo har mun shiga aiki. Ance yau ango zai shigo ɗakin Amarya ai gara mu samu mu kammala komai a nitse. Kinga wasu fararen labulaye masu kauri dana siyo inaso ko yayane mu raba ɗakin biyu ta yadda ko an shigo ba za,a ga wanda ke kwance a gado ba ko ya kika gani?" Lallai wannan dabarace mai kyau na kuma ji daɗinta sosai na baku wuƙa da nama" Anti Ramata da Cubu kuma kujeruna suka fitar dukka waje muka haɗu muka sake ma ɗakin fasali babu laifi yafi na farko kyau. Kujerar doguwa guda ɗaya kaɗai aka mayar, sauran nace Baɗɗo ta ɗauki 2 sitter ɗin sauran 1_1 ɗin akai gidan Dada a ajjiyema Cubu in aurenta ya tashi sai a kai mata. Muka gyara komai abincin gara na ɗebi wanda zan ɓoye na tura ƙarƙashin gado, dama na sai maggi dunƙule katan guda, na daka yajin barkono da yajin daddawa, na sai kayan tea na dayawa, na sai tocilolina masu batura hatta baturan na sai abina, Uwani tayo mun miya, mun tawo da risho da kalanzir, ƙananun abubbuwan buƙata dai wanda nasan zanyi amfani dashi duk na sai kayana na adanasu. Cikin awa uku ɗaki yayi shar dashi gwanin ban sha'awa. Mata masu zuwa ganin ɗaki har daga maƙotan ƙauyan zuwa sukaita yi basu taɓa ganin kaya irin nawa ba, yadda aka raba ɗakin biyu shima ya burgesu sosai. Haka dai aka wuni cur ana sha'anin biki. Wuninnan cur kuwa ruwa akaita makawa. Sai magriba ruwannan ya tsaya na samu nayi wanka na sake kwalliya. Anayin isha su Uwani suka watse suka barni ni kaɗai a ɗakin ƙwalam akan kujera na ƙurama tocila idanu. Ɗaga kai nayi na kalli yadda su Uwani suka rufe azarar saman ɗakin da farin labule cikin hikima. Na daɗe a zaune ina karanta wasiƙar jaki ga turaren tsinke sai ƙamshi yake fitarwa daga saudiyya na siyo. Wajajen goman dare har bacci ya soma surata akan kujera na jiyo shigowar Yaya Hamma. Da sauri na buɗe idanuna dan na tsorata sosai. "Tsoro kikaji ne Jabu naga kin tashi a zabure?" Saye yake da wani yadi green yala_yala ɗinkin ƴar shara, kanshi babu hula sai suma data zame mai ado ta kwanta ta laɓe a dogon wuyanshi. Sai ƙamshin turaren sasarobia yake yi, hannunshi riƙe da leda mai zane" Da sauri na miƙe tsaye ina shirin amsar ledar hannunshi. Saijin hannunshi nayi ya riƙe ƙuguna ya jawoni na faɗa jikinshi. Ƙam ya riƙeni, nima na riƙeshi ta baya riƙo na ƙwarai. Munkai kamar minti biyu cur muna shaƙar numfashin junanmu. Ni dai wani abune ya shiga yi mun yawo tun daga dunduniyata har zuwa kaina. Ji mukayi an bankaɗo labulen ɗakin an shigo. Ga wani irin kukan jinjira na fitar hayyaci. Da sauri muka saki juna. Hama ce a tsaye riƙe da jaririyarta dake canyara kuka. Wuf Hamma ya amshi yarinyar yana tambayar Hama meke damunta. "Baccinta take yi lokaci ɗaya saita soma firgita tana zabura tana miƙewa, sai kuka ka dai ganta" Jijjiga yarinyar ya dinga yi, amman yarinyarnan kamar ƙara zugata akeyi sai canyara ihu takeyi bakinta na rawa. Kafin kace me matan gidan duk suka yo ƙofar bukkata suna tambayar ba'asin wannan kukan. Hamma ne ya fita da yarinyar rataye a kafaɗarshi. Ina jiyoshi yana musu bayanin da Hama tayi mishi da fulatanci. Ni kuwa ina tsaye a inda suka fita suka barni, ga ledar kaji tarwatse a ƙasa. Tun inajin muryoyinsu harna dena jiyowa, kukan yarinyar yayi nesa sosai. Wallahi saida nayi awa guda cur a tsaye in kai mari in kai gwauro ina tubkewa da warwarewa. Labulena aka ɗaga Hama ce fuskarta a sake tace. "Amarya sai haƙuri auren mai mata angone yace in sanar miki zamu kai yarinya gidan magani, wai ki kwanta kiyi baccinki, in mun dawo zai kwanta a ɗakina sabida jikin yarinyar" Numfashi naja sama nace. To Ubangiji Allah ya bata lafiya, gaskiya ya kamata ya zauna tare daku har sai ta samu sauƙin jikin nata" Labulen ta sake. Ni kuma wasu siraran hawaye suka gangaro a kumatuna lumshe idanuna nayi na kaɗa kaina na zauna a kan gado ina karanta wasiƙar jaki. In ƙulla fari in ƙulla baƙi zuchiyata bata gamsu da kukan yarinyarnan ba wallahi. Duk da naga yadda take kukan fitar hayyaci. Amman babu komai ai hama ba zata dauwama tana cin nasara a kaina ba. Wannan dai ta shammaceni. Bari mu gani gobe kuma dame zata zo. Kwanciya nayi ina kallon sama sanyi na ratsani. Irin wannan weda ta ma,auratace, naso yau yadda wedarnan ta bada haɗin kai mu raya wannan dare. Amman babu damuwa gobe ma ranace. Da tunane_ tunane bacci yai awon gaba dani mai cike tab da mafarkai marasa daɗi. Ƙarfe ukun dare na miƙe a bahun na ɗaura alwala na soma sallar nafila har zuwa ketowar alfijir. Saida na sallaci asuba na kwanta a kujera dan tsabar bacci kaina kamar zai fashe. Kamar a mafarki nake jiyo muryar Baɗɗo da Uwani a kaina. Ina buɗe idanuna ilai kuwa sudinne. Uwani riƙe da takaddar kajin da Hamma yai watsi dasu. "Iyabo ya kaza haka a yashe a ƙasa ga Amarya kuma akan kujera, Allah yasa lafiya?" Uwani ta tambayeni. Sai da nayi Ajjiyar zuchiya kana nace. Ina kuwa lafiya Uwani. Har ɗaki aka shigo aka janye ango har yanzu banma sashi a idanuna ba. Ke jiya ni naga bariki." Shewa Uwani tayi, ta nemi waje ta zauna niko na labarta mata halin da ake ciki. Hararata tayi tace. "Kin bani kunya. Karfa ki bari zaman saudiyya da kikayi ki bari ya tashi a banza. Wacce yaudarace baki gani ba. Ga zaman gidan Gwadabe wanne siraɗine baki tsallakeba? Ko da yake nifa Hama burgeni tayi, ai baki ga komai ba Iyabo" To Uwani ya zanyi ni mamakine ya hanani kataɓus. Amman bawai zan bari ta takani yadda taso bane sam. Jiyanma ta shammacenine wallahi. Na kuma barta ne kawai in halinta ne zata sake. Zigata akeyi shi yasa duk take wannan abubbuwan." "To gaskiya karki sake bari hakan ta faru. Yanzu dai wannan kajin ai sai mu zauna muci mu kora da lemu rabonmu ne" Wanke bakina na fito nayi a ƙofar ɗakina na koma ciki, muka zauna mu uku saida muka ta da kajinnan biyu ƙananune sosai muka kora da lemun kwalba. Ko da aka kawo mana ɗumamen tuwon masara bamu ci ba mayarwa mukayi. Rishona na fitar ƙofar ɗaki na dafa ruwan wanka nayi, na sha kwalliyar les fari tas. Su Anti Ramata ne suka shigo da shirinsu na komawa gida tsab. Nasiha suka sake yi mun dai a gurguje. Burodami Kokodeen ma ya shigo yai mun nasiha suka kama hanya. Haka dai muka wuni a ɗaki maƙota sai shigowa ganin Amarya suke yi ba ƙaƙƙautawa. Da rana Hama ta girko shinkafa da miya aka kawo mana, miyarnan baƙi sosai kamar anyi sauwarta da ruwan rubutu. Daga ni har Uwani bamu ci ba. Yafendo ce ta aiko mana da fura da yawa. Dada kuma ta aiko mana da farfesun kaza, shi muka ci muka ƙoshi. Wajajen azahar yaran Baffa Musa, da yaran Yafendo A'i, da su Karima harda Daso duk suka taru akaita hirar zumunci. Mafi yawan hirar da fulatanci suke yi sai hausa jifa_jifa. Daso dai ba komai take sa musu baki ba, niko na sake sosai a cikin ƴan uwana. Sai da sukai sallar la'asar sannan ko wacce ta kama hanyar gidanta. Ritsona na fitar gefen ɗakina na ɗaura ruwan zafi. Uwani ta shiga gyara mun ɗakin dan duk ya hargitse. Ruwan zafin na tafasa na cika filasaina du biyun na sake mayar da wani ruwan na wanka. Kafin ayi sallar magriba na fito daga wanka. Saida nayi salla kana nayi zaman dirshan na shafe jikina da mai, nayi kwalliya mai sauƙi na sanya doguwar rigar yadin boyel me ruwan baƙin bulu ( blue black). Na saka ɗankunne da sarƙata fashion ja kasancewar akwai ƙaramin keb a wuyan rigar boyel din anyi da jan zare. Na feshe jikina da turare shar. "Bari in nemo miki gaushi ki soma amfani da turaren wutanki ɗan saudiyya wallahi ba dai ƙamshi ba." Fita tayi da kaskon turaren wutan. Tana fita Safiya matar ƙanin Hamma ta yo sallama ta shigo hannunta riƙe da langar tuwo da miya ta ajjiye. "Ga abinci Adda Jabu. Baɗɗo har yanzu bata gama girki ba shine nace bari in kawo miki" Murmushi nayi mata nace. To Nagode kwarai Safiya" Tana fita uwani ta shigo da gaushi. "Gashi kishiyarki ce ta bani. Kinga wata yaluwar atampar data saka wai ita tayi kwalliyar yamma? Wuyan rigar baya ko zama tsabar yadda yayi mata yawa, ta ko rambaɗa jar hoda fuskarnan tayi jawur." Dariya muka tuntsire dashi. Baɗɗo ce ta shigo da tiran abinci. Shinkafa jallof tayi da kifi, sai fura da dambu cikin jug ɗin silba. "Adda wannan nono da Dambun na Yaya Hamma ne. Kullum sai ya sha babu fashi nasan baki sani ba shine nayi miki. Ga abincinku. Adda Uwani muje muci namu Yaya Hamma ya dawo yana wajen shanu" Kwanukan abincin Safiya na mika ma Baɗɗo. Ungo ko yaranki sa ci, wannan ya isheshi ni a ƙoshe nake" Ta karɓa suka fita. Suna fita na ta da sallar Isha. Ina zaune ina lazimi Yaya Hamma ya shigo da sallama hannunshi riƙe da baƙar leda babba. Da sauri na miƙe na amshi ledar hannunshi na ajjiye a gefe. Zama yayi a kujera yana sauke ajjiyar zuchiya da gani a gajiye yake dan idanunshi sun lumshe da ƙyar yake buɗesu. A gefenshi na zauna. Sannu da dawowa Yaya Hamma " Hannuna ya riƙo ya matse a nashi, ya zuba mun idanunshi da yake lumshesu. "Amarya kinyi kyau. Ɗakinki yayi kyau sosai, tsarin ya burgeni" Murmushi nayi mishi kawai. Ina ka shigane tun jiya rabona dake. Murza hannuna yayi yace. "Ke dai bari, yadda naci burin daren jiya bai kasance yadda na tsarashi ba. Yarinya ba ita ta samu bacci ba sai asuba, ina dawowa masallaci kuma na wuce gidan Baffa Musa yana nemana. Acan na daɗe daga nan kawai saina wuce wajen aiki dan nasan gidan cike yake da mata. Aimun afuwa in ran gimbiyata ya ɓaci, ba da nufi komai ya faru ba. Su Inusa ma ƙorafi suke yi mun wai ban kawosu sunci tuwon Amarya ba" Ɗan murmusawa nayi nace. Ai babu komai. Ciwo ya doke komai ai, ciwonma na yarinya ƙarama. Su Iyaa sun tafi yau, uwani kuma sai jibi so take tabi Baɗɗo suje cin kasuwa akwai abubuwan da take son ta sassarane" "Uwani baiwar Allah. Wannan ƙawancan naku yana bani sha'awa gaskiya. Ina muku fatan ya dore har ku haɗa ƴaƴanku auratayya" Ameen. Yanzu dai me kake son ka soma, wanka, ko cin abinci? Naji sai warin rana kake yi" Duk wannan hirar a shingiɗe yake a kujera hannuna yana cikin nashi yana murzawa. "To wanne kika ga ya dace dani? Ni wanka ai sau ɗaya nake yi, wani sa'inma sai in kwana biyu gaskiya banyi ba, sabida yanayin aiki da kiwo" Dariya nayi, shima dariyar yayi yace. "Sai kinyi haƙuri mijin naki ƙazami_ƙazamine" A'a ba haka bane. Kar ka damu wannan duk ya kau daga yau. Wanka sau biyu safe da dare in sha Allah. Bari in kai maka ruwan wankan ka watsa sai kazo mu ci abinci, ga nono da dambu yana jiranka" Ina faɗin haka na miƙe na juye ruwan filas ɗaya a bokitin ƙarfe, na fita waje randata tana bakin ƙofata na surka mishi ruwan, na haɗa mishi da soso da sabuluna na kai mishi. Yaje yayo wankanshi tsab, na dangwalo mishi dakakken gawayi wanda aka cakuɗa da alim nace. Goge bakinka tas Yaya Hamma " Murmushi yayi ya amsa ya tsugunna a ƙofar ɗakina ya jima yana goge bakinshi. Ni kuma ina ciki na haɗa mana tea na zuba mana abincin Baɗɗo. Na zuba miyar stew da uwani tayi mana taji soyayyan kifi sukunbiya. Tare a plate ɗaya muka ci abincin, kaɗan yaci ya ɗauki nono da dambu ya sha, ni kuma na sha tea. "Akwai kazar amarci a ledar dana shigo da,ita ki ɗakko" Ai sai dai da safe mayi karin kumallo da'ita a yanzu gaskiya na ƙoshi. Gaga_gaga muka kammala duk abinda ya dace, muka ɗauro alwala muka yi sallar nafila bisa Shari'a. Daga nan al'amura suka soma sauya salo, daga ƙasa zuwa kan gado. A hankali abubbuwa masu daɗi da wuyar fassaruwa sukaita gudana. Har abinda aka daɗe ana mafarki ya tabbata a tsakaninmu. Abinda ya curemu muka zama guda kenan. Abinda ke ƙara soyayya da shaƙuwa a tsakankanin ma'aurata. Yaya Hamma yayi mun bazata, dan banyi tunanin tattali irin wacce na samu ba, asalima ban kawo irin wannan tattalin ga mutumin ƙauye ba, sai gashi ya kere tunanin Iyabo. Dan wallahi Gwadabe da wasa bai taɓa kaini irin wannan duniyar ba. Shima kuma na fahimci na kaishi duniyar da babu fulani a cikinta. Wannan yanayin ya ƙara mana so da shauƙin juna sosai. Bayan komai ya lafa muna kwance muna mayar da numfashi, Yaya Hamma ya juyo ya zuba mun idanunshi masu haske kamar madara. Abu ɗaya da ya bani tsoro shine na fahimci Yaya Hamma kamar baya aski ko ince baima taɓa yi ba irin yadda na fahimci yawan gashin. Amman nasa a raina zuwa washe gari zai aske shi tas. "Jabu soyayyarki ta kasance ta daban a zuchiyata. Kin kafa babban tarihi a wannan daren mai ɗumbun nasara da tarihi. Allah yayi miki albarka. Nagode da kika tallafi soyayyata baki hofantar dani ba. Wallahi Allah shine shaidata da ban sameki ba, komai zai iya faruwa dani, ina nufin komai. Ina roƙonki komai sauyin yanayi dana zamani kar ki gujemun, kar ki juya mun baya" Mun jima a wannan daren muna ma junanmu alƙawarurruka masu nauyi da girma. Daga ƙarshe tare dashi muka je banɗaki mu ka yi wankan Sallah. Duk da yana noƙewa tare da jin tsantsar kunyata, har rufe idanunshi da tafukan hannunshi ya dinga yi. hakan bai hanamu yin nishaɗi ba. Yanayi ne mai kyau, irin yanayin da na jima ina mafarki kenan Allah baisa na samu tare da Gwadabe ba, sai gashi na samu a wajen Yaya Hamma. Bacci mu ka yi mai daɗin gaske, baccin da saura ƙiris Yaya Hamma ya rasa sallar asuba. A gurguje ya zura rigarshi mai warin hammata da warin awaki ya fita. Idanu na lumshe tunanina yana mayar dani daren jiya da ni'imomin dake kewaye da daren. Marata na shafa ina fatan Allah yasa Yaya Hamma yayi ajjiyar jininshi a marata in haifa mishi kyakkyawan santalelen saurayi me kama dashi ya samu abokin shawara. Da ƙyar na fito nayi alwala wani irin muƙu_muƙun sanyi ake busawa sosai. Ina idarwa na kunna risho na dafa ruwan tea na zuva a filas na ɗakko wannan kaza na ɗorata akan plate. Na mayar ma da Yaya Hamma ruwan wanka. Yana shigowa na kai mishi ruwan wanka, ya tafi ya yo wankan. Ni kuma na shiga cikin gidan. Matan gidan duk suna kitchen ɗin tsakar gidan ko wacce girki takeyi a murhunta. Wani irin murhu garesu ginanne mai kyau, da laka ake ginashi, sai ɗan ramin dora tukunya. Duk ramuka bibiyu akaima ko wanne murhu, nawa yana kusa dana Hama sabo dal dashi har fenti akeyi mishi. Ɗakin Yafendo na shiga muka gaisa sannan na fito na nufi kitchen din. A dokin ƙofar kitchen ɗin na tsaya. Hama na dafa madarar shanu ta ɗago muka haɗa idanu. Ta wani turɓune fuska wuyan rigarnan nata a sauke nonuwanta rabi da kwatansu duk a waje. Wani tsohon kitsone a kanta duk ya furje. Ga gashi dai yala_yala amman babu gyara duk abun katifa ya rirriƙe gashin haka ma kan yaranta yake. Babbar ƴarta me sunan Yafendo tana gefenta riƙe da kofi hancinta sai yoyyo yake yi. Duk sanyin da akeyi kan yarinyarnan ba ɗankwali, ƙafarta babu takalmi ba suturar arziki. Maman Dada ina kwananku? Hama ta juya kai ta mayar da hankalinta akan madarar da take dafawa. Sai su Fatu da Safiya ne suka amsa muka gaggaisa. Baɗɗo ta gaisheni tare da cewa. "Yanzu nake son in kawo muku madara ku karya" To sai in tafi da'ita. Maman Dada kayan Yaya Hamma zaki bani yayi wanka yana son sauyawa" Sai ta saki muciyar da take juya madara ta juyo a fusace. "Shine ya aikoki ko zuwa kikayi ki sanar dani ya kwanta dake kome kike nufi Jabu? To bazan bayar da kayan ba shi bashi da ƙafar da zaizo ya ɗauki kayanne." Taja dogon tsaki ta fice fu a kitchen ɗin, saida taso bangazata na matsa da mugun sauri. Dariyar Uwani na jiyo daga bayana. Harda tafinta Uwani ƴar duniya kenan. Nima darawa nayi kawai. "Sai haƙuri Jabu. Yanzu Maman Dada a cikin fishi take" Cewar Safiya wacce na lura tana da hankali. Ba komai Safiya komai zai daidaita. Baɗɗo bani madarar" Madara ta miƙomin cikin kofin silba na nufi inda Uwani ke goge bakinta. "Wannan kishiya taki sai kinyi da gaske. Irin wannan daga miki murya da take yi haka, sai kace uwarki?" Ke dai bari Uwani. Bari in sallami Yaya Hamma zan zo in sameku, ƙila ma muje kasuwar tare in ya barni dan inason in yi siyayyar kayan miya da abinda ba za'a rasaba ƙila yau muna da baƙi masu cin tuwon dare. "To Shikenan sai kin shigo maza aje a kula da megida" Komawa nayi ɗaki na tarar da Yaya Hamma yana karyawa. Harka soma karyawa Yaya Hamma? Murmushi yayi mun. "Na gama ma. Inaso in fita kiwone yau nama ɓata lokaci sosai." Kallonshi nayi ya miƙe tsaye nace. To Allah ya tsareka ya dawo da kai lafiya. Yauwa Yaya Hamma nace abokan naka su nawa ne zasu zo zan musu girkinne?" Hularshi ya mayar kanshi kana yace. "Mu shida ne." To dan Allah inaso zan raka Uwani kasuwa siyayyarta da yawa kuma nima ina buƙatar zan ɗan yi siyayya". Jim yayi kamar bazaiyi magana ba dai. Sai yayi dariya kuma yace. "Da ƙafa suke zuwa cin kasuwar fa, mota wuya take yi sosai in zaki iya to kuje sabida dai Uwanine amman da bazaki ba" Nera ɗari biyu ya bani yace. "Ga kuɗin cefananki nan sai ki sai abinda zaki siyo acan yafi arha. Ki karɓi garin tuwo da ɗanyan man shanu a wajen Hama zan mata magana ta baki" A gurguje mu kai sallama ya fice. Kayan karin na tarkata na fito na nufi tsakar gidan. Yaya Hamma yana ƙofar ɗakin Hama da sandar kiwonshi, mijin Baɗɗo kuma yana kaɗa shanun waje. Bance musu um ba na wucesu kamar ma ban gansu ba. Tare da su Baɗɗo muka ci kazarnan da tea muka kora da dafaffiyar madara. "Bari inje in harhaɗa kayan nonona sai inzo mu tafi Adda Uwani" Fita tayi, fitarta ke da wuya uwani ta soma zolayata. Da dariya na bita kawai. Baɗɗo ta gama haɗa ƙorenta na Nono ta leƙo tai kiranmu akan muje. Muna fitowa Hama na ɗaura ƙoren nononta a ka, ta fice tana tsaki. Yafendo muka je mu kaima sallama. "Jabu har da ke za'aje?" E Yafendo inaso inga kasuwarne" na bata amsa ina sauke kai ƙasa. "To Shikenan. Nima yanzu ina gamawa zan biya ta wajen Adda Daso kafin in wuto kasuwar." To Yafendo muma in muka dawo zamu biya can uwani zata maata Sallama. A wannan kasuwar naga tarin ƙauyawa iri da kala. Ga masu tuyar ƙosai da masu saida burodi, komai akwai a wannan kasuwar gasu da arhar nama, ga kayan hatsi, gasu nono, mam shanu, madara, suturu, harda shanu da tumakai, kaji, zabbi, rediyone tocila, su kayan miya ɗanye da bushasshe babu fa abinda babu. Ga maza da matan Fulani damƙam wasu sunzo siyayyane irinmu, wasu kuma kasuwanci ya kawosu irinsu Hama da Baɗɗo. Haka mu ka shawo siyayya nan muka baro Baɗɗo. Bayan mun dawo muka ya da zango a gidan Dada anan muka tarar mai nagge yazo ya tusa ƙeyar su cubu yace ba zasu zauna a hannun Dada ba. Su Baffa Musa suna zazzaune ana mayar da zancan Dada sai hawaye take yi muka shigo. Baffa ne yai mun bayanin halin da ake ciki, da korar Amaduyal da yayi a gidan nashi kan yace bazai iya dena zuboma Dada abinci in matarshi ta dafa ba. Shine ya ƙwace shanayen dake hannun Amaduyal ɗin ya fito musu da kayansu. Ajjiyar zuchiya na sauke bayan na gama jin komai nace. To babu damuwa, su Cubu su je su zauna wuya bata kisa. Amaduyal kuma ga ɗakinan ku share kai da matarka ku zauna. Shanu dama ina da burin siya ko babu yawa zan danƙama ka dinga yi mun kiwonsu, a jiki ku dinga samun madara, nono da man shanun da zaka kula da iyalanka da abincin da Dada zata ci. Dada ki dena kuka Allah zai rufa mana asiri." Baffa Musa ya sauke ajjiyar zuchiya yace. "Shikenan an samu masalaha. Jabu sannu da zumunci Allah ya baki waɗanda zasu yi miki kema. Mai Nagge kuma ina ƙara jan kunnenki kar ki kuskura wani abun ya shiga tsakaninku, ko bayan raina kar ku tayar da maganar shanun Daso daya danne ya zama mallakinshi mugun mutumne wanda zai iya kashe duk wanda zai tayar da wata magana akan shanunnan. Duk shanun da kikaga yana gadara dasu na Daso ne wanda ta samu a gado, labari aka bani rugga_rugga sai yawon bin bokaye yake yi kuma duk akan a rufe bakinmu kar mu tada zancen Shanu ne. To mun yi shiru zamu haɗu a gaban Allah" Ba komai Baffa mun bar maganar in sha Allah. A dai nema mana shanu sai mu siya manya da ƙanana sabida shi Amaduyal ya soma fita kiwo, duk da gidan babu inda za'a iya garke. To anan nake cewa daku mu tara ranar monday in Allah ya kaimu. To ina ƴan team Hamma goga dai ya ciri tuta. Ina masu ƙin Hamma me zaku iya cewa ina sauraren ra'ayinku. Mrs Bukhari Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (4) Maraɗi. Robar ƙarin ruwane ɗaure a hannun malam, numfashinshi yana sauka da hawa a gurguje sosai. Daktar ne tsaye a kanshi yana ma ƙarin ruwan dake ɗaure a hannun malam allura. Tasi'u da Jamilu ne a kusa da malam kusan a tsaye suka kwana akan malam. Iyayensu kuma a zaune a ƙofar ward ɗin suka kwana ciki harda Baba Suwaiba wacce ta zama itace ummul aba'isin faruwar komai. Kafin ƙarfe bakwai na safiya iyalan Malam kab sun hallara, ko wacce uwa na zaune a gefe guda da bataliyar yaranta a gefenta. Tsakanin Amaryan malam, Baba Suwaiba, Baba asshi babu komai face harara da jan dogayen tsaki. Yaran maza da mata sunyi tsit kamar ruwa ya cinyesu kowa da tunanin da yake yi. Buɗe ƙofa akayi gadon jan marasa lafiyane ya fito malam na kai baisan a wacce duniyar yake ba. "Ina za'aje dashi wannan yaron?" Baba Fhatsima ta tambaya a tsorace. Hawaye Yaya Tasi'u ya share yace. "Na nemi a sake mishi ɗakine, sannan Malam yana bukatar adda'ar matanshi da yaranshi. Auwala ku haɗu dukkanku ban ware kowa ba aje a sauke ma malam Qur'ani ayi sadaka." Hawayenshi ya kuma sharewa yabi bayan ma'aikatan jinyar a baya. Jamilu kuma ya tsaya tattsunawa da uwarshi da ƙannenshi. "To ai kowa yaji abinda Babban wa uba yace. Sai mu tafi ai ko?" Cewar Auwala kenan. Buɗar bakin Muntari sai cewa yayi. "Ni babu inda zani, ku dai da kuke tunanin Malam ku kaɗai ya haifa, kuma uwarku mowace sai kuje kuyi mishi" Yinƙurowa Auwala yayi kan Muntari da zafin nama. Da sauri Baba Suwaiba ta miƙe ta shiga tsakankaninsu. "Kul Auwala karka sake ka tayar mana da fitina a wajennan. Ka barmu muji da bala'in da uwarku ta jefani a ciki. Saukace dai yace bazaiyi ba ku da kuke jin zaku iya kuje ga hanya" Saroro yaran suka yi suna kallon Baba Suwaiba. Ɗaya bayan ɗaya suka shiga zamewa suna ficewa. Banda yaranta su suna zaune tare da'ita. A mota Hadiza sai kuka take yi na baƙin cikin irin zaman da akeyi a gidansu. Wannan rayuwa da muni take, Malam na da rai ma kenan kai yaƙi haduwa ina ga Malam ya bar duniyar kuma, yaya gidan zai kasance ina makomar zumunci tsakankanin ƴan uwan junan?" Gwadabe ya dafata yace. "Hadiza wannan kukan ya isheki haka. Malam adda'a yafi buƙata, Allah zai tashi kafaɗunshi." Auwala dake gaba a zaune ashe shima hawayen yake yi yace. "Ka barta ta koka irin rashin haɗin kan gidanmu Gwadabe. Nima kukan nake yi, ace mahaifinka yana kwance rai a hannun Allah. Amman kai bata lafiyarshi kake yi ba. Kaji fa abinda Muntari yake faɗi. Kaji irin goyon bayan mahaifiyarshi. Me Malam yayi daya cancanci irin wannan hukuncin daga diyoyinshi?" Idanu Gwadabe ya lumshe, rayuwar gidansu na haskawa a kwaƙwalwarshi da irin tsanar da ƴan uwanshi suke mishi,hatta Babala bata fatan ta buɗe ido ta ganshi. Ai halin da yake ciki akan danginshi yafi nasu ciwo. Matsalolin ƴan uba abune sananne wanda yazo a cikin tarihin Annabi Yusuf da ƴan uwanshi suka zaɓi jefashi rijiya, sabida ƴan ubanci, da zafin nuna fifiko" Amman tashi matsalar mai rikitarwace sosai" "Auwala ayi haƙuri komai ai mai wucewane wata rana sai labari. Duk daren daɗewa abubbuwa zasu zo suyi sanyi kuma su warware. Fatanmu Allah ya ba Malam Lafiya" Haka suka ci gaba da tattauna manyan matsalolin gidan har suka iso gida. Ayau dai su Sabitu babu fitina har aka kammala saukar Qur'ani kasancewar tare da manyan gardawan malam aka haɗu akayi sai abun bai ja lokaci ba aka kammala. Su Auwala ana gamawa suka sake komawa Asibitin. Su Hadiza kuma suka tsaya girkin abincin da zasu kai asibitin. Sha biyun rana Hadiza ta gama lafiyayyen tuwon shinkafarta miyar kabewa yaji naman rago. Ta jera komai a babban basket ta fito. Daidai fitowar Shafa itama a shirye take tsab tanaso zata bi Hadiza asibitin taga halin da me jikin yake. Tare da Anti Badi'a suka dunguma suka tafi. Acan suka tarar da Matar Jamilu. A wajen wata baranda suka shinfiɗa kapet huɗu, ko wacce mace da yaranta mata da ƴan uwanta. Haka abinci ma kowacce nata dana jama'arta daban sabida tsabaragen rashin haɗewar kai. Sai da yamma Yaya Tasi'u ya leƙo yace. "Baba kizo Malam ya farka sai ambaton sunanki yake yi." Da sauri Baba Fhatsima ta miƙe, Baba Asshi ma ta miƙe ta bi bayan Baba Fhatsima" "Baba kaɗai yace yana son gani. Dan Allah Baba Asshi ki koma kar ganinki ya ɓata mishi rai" Cewar Yaya Tasi'u, cikin girmamawa yayi maganar. Ita kuma cikin hargowa tace. "Ko tare da uwarka kake yawo baka isa ka hanani shiga ɗakin mijina ba. Kisa ya sakeni kamar yadda kikai sanadin fitar Suwaiba" Ta dubi Baba Fhatsima tana harararta. Murmushi tayi kawai. Ta girgizama Yaya Tasi'u kai halamun yai shiru. Tare su ukun suka shiga ɗakin da Malam yake kwance. "Asshi kar ki shigo inda nake. Ban kiraki ba bana buƙatar ganinki. Tasi'u ka fita da'ita in dai ba kana daga cikin masu son in mutu suci gadona bane" Turus Baba Fhatsima da Baba Asshi sukai a tsaye a ƙofar ɗakin. An rasa me shiga, da me fita. "Bakomai Malam, ba dai ni ka jefa da wannan furucin ba? Daga ni har ƴaƴana babu wanda zai sake tako ƙafarshi yazo dubaka. Da sakina kayi na huta da baƙin cikin Fhatsima data kwashe shekaru tana ƙunsa mun" Tana gama faɗar haka ta fice da kuka nan ta tattare kan yaranta tana kururuwa suka fice daga asibitin. A ranar ta sanar ma ƴaƴanta duk wanda ya sake shiga harkar Baba Fhatsima da yaran ɗakinta bata yafe mishi ba. Wannan dalilin ya zama tsani na ƙullatar Baba Fhatsima da yaran ɗakinta. Baba Asshi ta haddasa gaba mai ƙarfi a tsakankanin yaranta da ƴan uwansu. Ƙafarsu bata sake taka asibitin ba har Malam ya kwana shida a asibiti jikin yayi kyau aka sallamoshi. Ko da aka sallameshi Baba Asshi da yaranta babu wanda yaje ya duba malam da jiki harkokin gabansu kawai suke yi. Ta ɓangaren Baba Fhatsima da Malam kuma. Haka taita tausarshi tana kwatanta mishi ba'a gyara ɓarna da zafi. Matakin daya ɗauka ba matakin gyara bane. Da ƙyar tun yana asibiti tasa ya dawo da Baba Suwaiba, da matar Malam ɗakinsu, kuma suka tare kafin a sallamo Malam ɗin. Zaman gida ba daɗi matar malam take ji ba. Baba Suwaiba kuwa sai yawo take yi a tsakankanin gidajen yaranta. Ta bangaren gidan Yaran Malam kuwa, babu jituwa a tsakanin matan gidan, sakamakon rashin haɗin kan dake a tsakanin mazajen nasu. Zuwa kwsnciyar Malam a asibity da sallamoshi suka san duk abinda ke gudana a tsakanin ahalin gidan. Lamarin sai ya zama yau in ba'ai hayaniya akan shara ba. Gobe akan wanke bayan gidan tsskar gidan za'ayi, gidan ya zama tamkar masu ganin hangin junansu. Ga gasa, ds yin bajinta a ƙoƙarin ko wanne ɓangare na son nuna shi ɗin shine. Malam ya ɗauki ido ya zuba, ya hana Yays Tasi'u cewa komai yace a barsu yana son ganin iyakarsu. Ta ɓangaren Hadiza da Shafa kuwa, babu yabo babu fallasa. Da safe kafin dukkanninsu su fita aiki suna haɗuwa su gaisa. Haka da daddare suna haɗuwa a ɗakin wacce bata da kwana aci abinci a ɗan taɓa hira kuma sai ku ma wacce akayi hira a ɗakinta sallama. Hadiza basa rabo da faɗa da Gwadabe dan ƙes ta gani wanda baiyi mata ba saita sashi gaba da maganar, hakan yasa ta zama mai yawan ƙorafi da yawan fishi. Saɓanin Shafa da take danne abubbuwa da yawa, kafin tayi ƙorafi sai abun yaci tura. Kwatsam wata ranar juma'a tun a makaranta Hadiza tai ta faman sheƙa amai dama kwana biyu bata gane kanta ba. Ya tabbata zargin tana da ciki ya tabbata. Ana tashi tayi gida dan zazzaɓi ne ƙaƙas ya rufeta. Tana zuwa gida ta kwanta gashi a ranar ita ke da girki, ta tashi ta dafa ta kasa, ta ce Shafa ta dafa kishi ya hanata. Sai ɓarayin Yaya Tasi'u taje Anti Badi'a ta cika mata babbar kula da farar shinkfa da romon gandar naman kan rago. Har Gwadabe ya shigo bata iya yin wanka ba, ɗakin nata ma bata yi shara ba, a haka ya shigo ya taddata a kwance a ƙasa. "Lafiya kike kwance a ƙasa Hadiza, ko dai babu lafiya ne?" Ya tambayeta bayan ya ajjiye mata kayan marmarin da ya zamar mata jiki shansu. "Wallahi jikinne sam babu daɗi. Kaga abincima sai ɓarayin Yaya Tasi'u naje na karɓo bazan iya girkawa ba" Kallonta yayi da kulawa, duk da yaji babu daɗi akan maganarta ta ƙarshe sai bai nuna ba yace. "Inane yake miki ciwo, kin kuma sha magani?" Dariya tayi tace. "Ciwon bana shan magani bane, ƙaruwa muka samu, ina nufin nan da watanni ƴan biyu zasu samu ƙani ko ƙanwa" Kabbara yayi tare da rungumeta cike da farin ciki yace. "Alhamdulillah dake da ƴar uwar taki ƙila babu nisa a tsakaninku. Itama kwanaki bata ji daɗi ba, sai ta shiga asibitin da take ba da kati aka mata gwaje_gwaje aka tabbatar mata tana da ciki" Sai Hadiza ta ɗan rage fara,arta. (Ku fahimta da Hadiza, da Baba Fhatsima wasu irin matane masu kishin sunfi son komai ace sune gaba. Bawai kishi take kar Shafa ta samu ciki ba, ta dai fi so ace itace ta soma laulayin kafin ita Shafar. Sai gashi a bayanin gwadabe da halama ɗanta ko ƴarta sai dai su biyo na Shafa, in ba wani ikon Allah ba.) Gaga_gaga lokaci yaita shurawa abubbuwa marasa daɗi sukaita faruwa, dambe tsakanin matan wannan gida, haka mazan dambe a tsakankaninsu. Zaman sulhu anyi yafi sau a ƙirga, haka zaman meeting ba'a denashi ba. Rarrabuwar kai sai sake ta'azzara yayi kamar yadda Baba Fhatsima da Yaya Tasi'u sukai hasashen haɗuwar ba lallai ta haifar da Alkhairi ba alai kuwa abinda ke faruwa kenan. Ƴan unguwa sunsa ma gidajen suna kusan kashi uku tsabaragen yadda suke shiga rabon faɗa a kullum. A haka dai akaita tafiya ranaku a cikin watanni. Har matan wannan gidan masifa suka soma haihuwa, duk taron suna sai anyi uwar watsin da kowa zai tafi rai babu daɗi. Jikin Malam kullum a cikin tashi yake, dan ashe a baya ba tashin hankali akayi ba, yanzune akeyi kunsan abu dama in aka haɗa da mata. Ana cikin haka wata safiyar talata Shafa ta haifo ɗanta namiji santalelen gaske, ta haihu da kwana biyu matar Auwala ta haihu itama, sai akace za'a haɗe bikin sunan. Hadiza kuwa jiki yayi nauyi sosai sai turawa take yi tana lallaɓawa a hakan ita take ɗorama Shafa ruwan wanka, Baba Fhatsima kuma ita ke ma jaririyar wanka Anty Badi'a kuma ita ke ma Shafa wanka, da ɗora ruwan wankan yamma, ana jibi suna ƴan takai suka iso harda Sakina da Toye akazo. Aka haɗu harda Hadiza akaita sha'ani tare da tsare_tsaren yadda sunan zai kasance. Ranar talata Yaron Gwadabe yaci sunan mahaifinshi aka mishi alkunya da Abba. Yaron Auwala yaci sunan Malam ana mishi alkunya da Magaji kamar yadda shima malam ake mishi alkunya da wannan suna. An gudanar da bikin suna lafiya za'ace kasancewar ba'ai wani taro mai yawa ba Shafa bata da dangi a ƙasar. Gwadabe yayi ƙoƙari ƙaton rago ya yanka ma mai jego, ga naman ƙauri saida ya kwana biyar yana kawowa ba tare daya gajiya ba. Kayan fitar suna Shafa kawai yayi ma kala biyu, ita Hadiza yace inta haihu zaiyi mata. Ita kuma atampa da rigar yaro mai tsada ta ba Shafa. A ranar suna da daddare gaga_gaga sai Hadiza ta kama ciwon naƙuda. Wasane gaskene taita abu guda Anty Badi'a na kanta har saida akai sallar asuba kana ta haifo ɗiyarta mace mai kama da'ita tamkar an tsaga kara." Da uwar da ɗiyar suna cikin ƙoshin lafiya. Hadiza tana yin wanka tasha tea sai bacci. Su Anty Badi'a da Ene data bugo sammakone suka kintsa wajen akaima jaririya wanka ta fito tubarkalla a cikin farin seti sai bacci take yi. Matan Auwala da Mammadane suka shigo barka, me jego tana kwance tana baccin wahala, har su Auwala suka shigo da angon ƙarni Gwadabe bata tashi ba. "Gwadabe an sake zama angon ƙarni. Gata ku ganta" Anti Badi'a ta miƙama Gwadabe yarinya ya amsheta da bismillah ya shiga yi mata adda'a, sai ga Ayashe da Sakina harda Shafa mai jego tana riƙe da jaririnta. Taiwo da Kahinde, da Toye suna biye dasu. Yaran da suka zamema Gwadabe sanyin idaniya, yaran da yake jinsu a ranshi fiye da komai da kowa. Baya jin akwai wani ɗa ko ƴa da matanshi zasu haifa mishi da zai sosu sama da nasu Toye sai dai ƙasa. Soyayyar babarsu tana nan a ƙasan zuchiyarshi. Yanayin jini da ya ga Taiwo sai yaga Iyabo sak, kuma dama yarinya jikinta irinna Iyabonne dan ƙiba gareta. "Shafa har dake a fitowa? Ai da kin zauna kema ba jegon kike yi ba" "A'a Anty ai babu komai nazo inga ƙanwar Abbane, in ma Maman Abban barka" Ta faɗa da fara'arta. Anty Badi'a ta karɓi Abba a hannunta. Aka gaggaisa duka su Sakina duk sukai ma Gwadabe da su Anty Badi'a barka. Me jego bata san wainar da ake toyawa ba tana uwar ɗaku. "Me jegon bacci take yi. Amman inta tashi zan faɗa mata" Cewar Anty Badi'a. Gwadabe yace da Sakina. "Sakina zaman maraɗi ya ƙara kamaki dan sai anyi suna zaki tafi" Dariya tayi tace. "Ai nima haka nace. Duk da su Toye zasu koma makaranta, amman zamu zauna ayi suna damu" Aka ɗanyi wasa da Dariya dai, su Gwadabe suka tafi aiki. Mata kuma suka ci gaba da zuwa barka. Gaga_gaga haka akaita jego, kullum Gwadabe na siyo naman ƙauri itama yai mata na kwana biyar. Har ana jibi suna gwadabe bai sanarma Hadiza sunan da yaima yarinya huɗuba dashi ba. Da daddare bayan sun gama komai suna kwance suna hirar ma,aurata sai tace. "Nifa har yanzu baka sanar dani sunan yarinyarnan ba, ko nima sai ranar raɗin sunan zanji?" Ta ƙarashe tana dariya. Shi kuwa duk saiya koma kalar tausayi. "Dama tun ranar da nayi mata huɗubar nake ta tauna yadda zan tunkareki da zancan" Ai saita miƙe zaune ta ƙanƙance idanunta tace. "Kar kace da sunan tsohuwar beyerabiyar matarka kaima ɗiyata takwara?" Dama yasan za'a rina, baiyi mamaki ba. "E da sunanta nayi huɗubar ina fatan zaki amshi hakan. Nayi alƙawarin saka sunan nata ga ɗiya macce da zan samu ta fari....." "A'a Gwadabe mu bar zancannan dan narantse da Allah ba zaka ma ƴata huɗuba da sunan wata ba. Uwata na da rai ba'ai mata taƙwaraba sai tsohuwar matarka daka kasa mancewa da'ita" Take ranshi ya ɓaci nan suka haura shima ya farfaɗa mata maganganun da yasan dole ranta ya sosu. Ya suri fulo yayi ficewarshi zuwa falo. Ya barta a gado tana risgar kuka wiwi kamar wacce aka aikoma da saƙon mutuwa. Wani irin muƙu_muƙun kishin Iyabo yaita fisgar ranta. Washe gari ta tashi cikin fishi da ƙuncin zuchiya. Haka ta wuni sukuku, zuchiyarta cike da fargaba kasancewar Gwadabe a ɗakin Shafa ya kwana sai su Sakina ne suka tafi ɓarayin Yaya Tasi'u suka kwana. Bata san ya canja sunan yarinyar ba ko yana kan bakarshi nasa mata sunan matarshi? Haka gari ya waye, ga mai jego taci kwalliya ta fito shar cikin shadda bazin wacce ta siya da kudinta irin adashennan da malaman makaranta ke kafawa, ta fito tayi ɗan karen kyau yarinya ma tasha ƴar kanti me riga da siket. Tsakar gida ta fito tanaso tayi magana da Anti Badi'a, nan kallo ya dawo kanta. Su Sakina suna bakin magudana suna aikin kayan ciki, Gwadabe ya shigo da ƙaton rago, Mammada na biye dashi da ƙatuwar tinkiya duk aka rataye mata a barandarta. Saita shiga mamakin shin rago biyu ya yanka mata kenan sabida yasa sunan tsohuwar matarshi? Ita kuwa taci alwashi in sama da ƙasa zata haɗe ɗiyarta ko sunan Shafa ba zata ci ba balle sunan tsohuwar matar mijinta, alo tsiya alo danja. Shafa ta fito daga ɗakinta da kayan Ƴan biyu itama sai taga raguna biyu a ƙofar Hadiza a rataye ga kayan ciki cikin ƙaton bawo su Ayashe sunata gyarawa. Masu yanka kabeji,da masu yanka kaji nayi gidan ya kacame da aiki da halama sunan na dabanne. Dan matan gidama sai ɗan fitowa suke yi gulma. Matar Mammada da Matar Auwala dake ɗauke da ciki na wata shida suma suna tsakar gidan suna aiki, banda ƙannen Hadiza da kawayenta duk kowa aiki yake yi, ga Hadiza ta sha Bazin asalin babbar me geza. Ƴan biyu dake guje_guje a tsakar gida Shafa ta kira da hannu, a guje suka isa gareta, ta jasu ɗaki Gwadabe ya bita da kallo dan yaga kamar akwai ɓacin rai tattare da'ita bazai wuce akan raguna biyu data gani ba, da suturar jikin Hadiza ba. Yana gama ratayewa ya nufi ɗakin Shafa ko kallon Hadiza baiyi ba. "Gwadabe mufa har yanzu ba'a sanar damu sunan wannan jaririya tamu ba" Anti Badi'a ta katse mishi hanzarinshi. "Sunanta Fhatsima. Alkunyarta Ummi" Ajjiyar zuchiya Hadiza ta sauke ranta yayi fes. Anti Badi'a ta saki guɗa tana faɗin. "Baba Fhatsima dole tayi mana fantimoti na takwara. Bari in shiga cikin gidan in sanar." Dariya Mammada yayi yace. "Sun rigaku jin sunan tun asubar fari ai. Sai dai in akwatin zaki karɓo" Dukkansu suka saka dariya. Gwadabe a bayan gidan Shafa yayi wanka ya kintsa, ya fito ya sameta tana wasa da ƴan biyu. "Shafa" ya kira sunanta, ta ɗago ta zuba mishi idanu ba tare da tace komai ba. "Raguna da kika ga biyu. Yaya Tasi'u ne ya ba Hadiza ragon ni tunkiyar na siya. Kar kiga tafi taki girma wallahi yanayine kawai duk da nasan tafi taki tsada. Suturar jikin Hadiza da hidindimun da kikaga anayi, wasu ita da kuɗinta tayi, wasu matar wanta Anti Badi'a mace mai karamci ce tayi mata. Kiyi haƙuri kinji ko, umman Abba?" Murmushi tayi, shima murmushin yai mata. "Babu komai Allah yasa mu dace. Haka dai akaita girke_girken suna a gidan abinci saida akayi kusan kala uku, ga cincin da alkali, harda soɓo da kunun gyaɗa duk saida akayi. Me jego da yarinya kuwa sunga gata sosai. Dan hatta Gwadabe kayan da Yaima ummi baima Abba ba, sai haƙuri ya ba Shafa akan zai ƙaro musu in ya samu kuɗi. Washe garin suna tun sassafe aka kafa kaskon suya. Su Sakina suka shiga shirin komawa najeriya, Hadiza ta ɗeba musu nama mai yawa sosai da cincin da dubulan. Baba Fhatsima kuma ta musu tsarabar lalle ɗan nijar mai mugun kamu da yankan salateb harda gishirin lalle wanda ake kwaɓawa da toka a shafa sai lalle ya dawo baki wudik. Har sun fita Gwadabe zai rakasu tasha sai ga wayar Tamu yana roƙon a bashi Shafa tazo tayi wankan gida. Tamu ya wuce ya nemi abu ya kasa samu a wajen Gwadabe. Babu shiri suka ɗaga tafiyar zuwa washe gari. Shafa saita shiga murna tana haɗa kaya. Gwadabe ne ya kai zancan gaban uwar ɗakinshi Baba Fhatsima. "To ai babu lefi tunda ka amince, kaga sunyi kawaici ma dan da wasu ne kafin ta haihu zasu zo su tafi da'ita. Babu damuwa Allah ya tsare" Ita ta sanar ma Malam washe gari suka kama hanya sai Najeriya. Kan Gwadabe ya ɗauki zafi dan a ranar yana da zuwa wani ƙauye cin kauwa zai kai magani ba ƙaramin ciniki yake yi ba. Sai ya sha'afa bai sanar da Hadiza batun zuwa wankan shafa ba sai a bakin Shafar taji da taje mata sallama. Alhamdulillah sana'ar saida magani tana kai mishi sosai babu laifi, har magungunan ƙarfin maza da su yaji dakan maza yake siyarwa, abu kamar wasa saiya soma haɗawa da ƙwayar bature duk dai na mazan. Kuma yana zaga ƙauyuka dan cin kasuwa, yana ciniki sosai babu abinda zaice da Allah sai godiya. Koda ya dawo ga gajiya, ga hayaniyar kasuwa saida Hadiza ta tareshi da ƙorafinta. "Ashe kasan Shafa ba zama tayi ba za'a tafi da'ita wanka shine baka faɗa mun ba." ( Mata mu dinga lura da lokacin daya dace mu shigar da ƙorafinmu ga miji. Kuma mu sani mu tsaya a iyakar matsayinmu dan kare mutuncin kanmu, musamman in kina da abokiyar zama) A faɗace yace. "Ai ba huruminki bane dan Shafa zata wankan gida saina sanar dake ba. Tunda ta miki sallama ai Shikenan. Da dawowata kin tarbeni da ƙorafi'" Yana faɗar haka ya shige ɗaki yana ta tauna al'amura lamarin Hadiza ya soma isarshi gaskiya mace sai shegen ƙorafi shi kenan kullum shi a cikin yin ba daidai yake ba kenan?" Tsaki yaja kawai. Gaga_gaga haka rayuwar taita turawa kwanaki cikin kwanaki. Har Shafa tayi arba'in. Ana gobe Hadiza zatayi arba'in Gwadabe ya dawo daga cin kasuwa can garin Tawa yace. "Ki shirya jibi zamu je Najeriya. Zamu je mu gaishe da su Babala da abokaina. Shafa ma jiya suka shiga Takai ɗin." "To Shikenan Allah ya nuna mana. Dan Allah kayi haƙuri a bisa laifin da nayi maka jiya. Wallahi zuchiyata ce ta kasa jura naga daka dawo a madadin ka mayar da hankalinka a kanmu ni da Ummi. Sai inga damuwarka Shafa dai da Abba." Ƙur ya zuba mata idanu kamar bazaice komai ba dai sai yace kawai. "Bakomai Hadiza. Gobe ma da ƙorafin da zaki kawo. Kinga ita ko Shafa bata taɓa mun ƙorafin komai a kanki ba. Hadiza baki gane bane kinci babban kaso a zuchiyata mai girma. Ya kamata ki kwantar da hankalinki" Murmushi tayi taji daɗi har a cikin ranta. Kuma ta gamsu da hakan. Tana girmama yadda Gwadabe yake ɗaga mata ƙafa. Har cikin ranta tasan kishi da ƙorafi shine matsalarta, tayi imani Shafa ma nada nata matsalar. "Na haɗa harda kason tsohuwar matarka na kwakwushe Iyabo?" MRS BUKHARI Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (5) Iyabo Baffa Musa yace. "Wajen kiwo ba damuwa bane. Ko nan gidanku zai dinga zuwa yana garkesu. Ko gidana, ko gidan me sunanki Jabu. Zamu bari ranar Talata ranar kasuwa sai muje akwai shanu na siyarwa da ake kawowa. In ma ba haka ba akwai inda zamu je da Amaduyal din mu samo miki. In yaso ko tunkiya da rago sai ke ki siya ki watsar a tsakar gida, suna cin ƙanzo da ciyayi sai kiga kin ta da garke, in wata matsuwa ta kamaki sai ki ɗaga abinki ki siyar. To Shikenan Baffa zuwa gobe Amaduyal zai kawo maka kuɗin in sha Allah. Duk yadda kudin suka yi sai ayi abinda ya dace dashi kuma zuwa jibi zan buɗe kayana in soma siyarwa, abinda na kuma gagganɗawa sai a sake siyowa, har kaji da zabbi inaso in saka, naga su Baɗɗo duk suna kiwonsu" Baffa Musa yayi mun dariya yace. "Jabu mutanen birni, ta dawo matar ƙauye" Nima dariyar nayi. Nan dai muka gama abinda zamu yi, zuwa bayan la'asar Uwani taima su Dada sallama akan gobe zata wuce, daga haka sai muka koma gida. Babu kowa a gidan, sai awaki da kaji da suketa shaƙatawarsu. Tsakar gidan duk datti da tarkacen bokatai da tukwanansu na dafa nono ƙudaje sai fareti suke yi. Mayafina na rataya a saman bishiyar gidan na ɗauki tsintsiya tun daga kitchen na zakulo shara, a iyakar kitchen kawai saida na fitar da tarkacen ledoji da toka ƙaramin buhu. Duk girman tsakar gidannan na share tas, na haɗe musu kayan kazantarsu a bakin rijiya inda suke wanke'wanke da wanki. Lokaci guda gidan yayi fes ras dashi. Karar girki dana gani a jibge a kusa da ɗakin Baɗɗo na ɗebo Uwani ta tayani muka hura wuta abu kamar wasa wuta ta kama na tsayar da sanwar miyata. Uwani tayi mun jajjage a babban turmin gidan, su citta, tafarnuwa, diyar miya duk muka daka na wanke naman rago na sashi a ɗayan gefen na murhun na sanar muku baki bibbiyu suke gina murhun, saina ɗaura tafashen nama a ɗaya, ɗayan kuma na tsayar da sanwar miyar karkashi. Awa uku cir muka yi a kitchen kafin na kammala tuwona na shinkafa miyar karkashi yaji nama. Soyayye Tuwon na ƙuƙƙula a leda na cika babban flaks, na bare sabon filas tuwo da miya na zuba na kai ɗakin Yafendo da dawowarta kenan. "Sannu Jabu gida yayi kyau sosai. Allah yayi albarka ya baku zaman lafiya" Ameen Yafendo nagode. Ina fitowa daga ɗakin Yafendo sai ga matan gidan sun dawo zuga guda da goyo da ƙananun yara raɓe_raɓe ga siyayya iri_iri sunyo. Suna ganin yadda gidansu ya sake sunsan aikinane. Sannu da zuwa nayi musu na shiga binsu da tuwon girma ɗaki_ɗaki. Da nazo kan Hama bari kuji abinda samodarar tace dani bayan taƙi amsar tuwon fur. "Au a rabe zamu dinga yin girkin? Aina ɗauka duk wacce miji yake ɗakinta ita zata girka abincin ?" Murmushi nayi mata. A'a ko wacce girkinta zata dinga yi, in ranar girkinki tazo kina wajen tallar Nono ni ina gida bazanci abinci ba kenan?" Ai saita zabura tace. "Ai kema zakiyi tallar nononne, wallahi ban yarda a raba girki ba" Dariya nayi mata na wuce da tunowa na ƙarama Baɗɗo. Bayan na fito wanka na zuba tuwon na aiki yaro ya kaima Dada dan nayi alƙawarin ko ƙasa na dafa tare zamu ci da Dada, kuma nasa Baɗɗo ma ta roƙi mijinta ta dinga aikama da Dada abinci duk a haɗu a rufa ma kai asiri. Yaya Hamma basu suka shigo ba shi da abokanshi sai bayan isha sai gasu. Naci dariya, sunyi santin tuwo sosai ɗaya daga cikinsu ma cewa yayi abincin ƴan aljannah ne. Sai tara da rabi suka yi mun sallama suka tafi suna faɗin zasu turo matansu koyon girki. Ni kuma sai nayi amfani da damar wajen tallata musu kayana tare da sanar dasu jibi zan buɗe dilar. Duk sunce zasu ba matansu kuɗi su zo su sai zanin gadon makka, kunsan dai kayan makka da farin jini. Bayan Yaya Hamma ya shigo mun kaɗaita komai ya lafa sai nake labarta mishi duk yadda muka yi da Baffa. Shima ya goyi bayan ayi hakan babu damuwa. Sai naji nasamu nutsuwa sosai. Washe gari sassafe Uwani tai mana sallama ta kama hanyar kano harda ƙaton zakaranta da Baɗɗo ta bata. Muna dawowa daga rakata ni da Yaya Hamma, yana shirin fita sai muka jiyo sallamar Amaduyal. Kuɗaɗen dake hannuna na tattare dubu ɗari ukku na bashi su a baƙar leda, ragowar kuɗaɗen dama nayi musu mugun ɓuya ƴan kuɗin hannuna bai wuce dubu saba'in ba haka wanda suke fili ɗan na zara a kashe wutar data taso. "To ni zan tafi aiki. Akwai abinda kike buƙatar in siyo miki a birni ne?" Ya tambayeni na girgiza mishi kaina. A'a babu sai dai in maka fatan dawowa lafiya. Amman kafin ka fita ya kamata ace akwai kayanka ko kala biyune anan ɗakin bawai kullum in kayi wanka zaka fita sai dai kaje ɗakin Hama ka saka ba" Dariya yayi ya shafa fuskata. "Hakane Jabuna. Zan ɗebo inna dawo. Kar ki manta kafin Hama ta fita ki je ki karɓo garin tuwo da man shanu. Inna dawo zan nuna miki naggenki da zaki dinga tatsar nono a jikinta, kinga sai Baɗɗo ta koya miki yadda ake fitar da man kya dinga fitarwa da kanki kin samu na girkin ki ko, madarar da Nono sai ki ta sha tunda kinƙi tallar nono " Dariyar soyayya mu ka yi ma junanmu. Na dinga ragargazo mishi adda'a yana ameen_ameen harya fice daga lungunmu. Sai da naga tafiyarshi ina rakuɓe a bakin lungun harya fita Hama ta bishi da gudu raɓe_raɓe da nononta guda ɗaya ta ciroshi ta wuyan riga. Ga Yuguda mijin Baɗɗo a wajen Hama ko a jikinta. Da ganin yadda take magana faɗa take yi ilai kuwa sai naga tana share hawayenta. Kaina na girgiza nayi komawata ɗaki nayi ɗaiɗai a ƙasa ina tura wainar ƙwai ina danne maiƙon da ruwan tea na me madara. Saida na gama karyawa na fita tsakar gidan, tun sassafe na kaima Yafendo nata abun karin. A zaune a ƙasa durshan na samu Hama tana jijjiga madara kwananniya dan fitar da man shanu. Kanta babu ɗankwali ya ilahi zo kuga gashi wallahi kamar a india amman annakiya zata kashe shi, wani irin dattine a daddanƙare akan da ciyayin katifa. Ina kwana Hama ya kwanan yaran?" Baki ta taɓe tace. "Lafiya" Dama Yaya Hamma ne yace ki bani garin tuwo da ɗanyan mai" Dariya tayi harda shewa tace. "Ai Hamma ya gama kwanaki ukkun da zaiyi a ɗakin ki, kinga harya faɗamun kalar miyar da zan kaɗa ta dare. Saiki bari in kwana ya zagayo kanki sai kizo in baki" Ta ƙarashe da Dariyar ƙeta harda sakin waƙa da fulatanci. Turus nayi a tsaye ina jujjuya kalaman nata. Taya akayi kwanan suka zama uku. Kenan harda darena na farko da tazo ta jaye shi harda daren a lissafi kenan? Wata bazawarar dariya nayi dan wallahi yau sai Hama taga bariki zan nuna mata nayi zaman gidan karuwai a saudiyya. Kaina kaɗa nayi tafiyata, matan gida sai kallona suke yi, Baɗɗo har ɗaki ta biyoni tana bani haƙuri ta kawo mun man shanu ƙwarya guda da garin jar masara nata. A'a ki koma da masarar, man shanun dai na karɓa." "Adda sabida ke fa ko gaisuwata Hama bata amsawa, ta hana yaranta wasa da nawa yaran. Ko a mota muka haɗu ta dinga tsaki kenan. Kuma ƙawayenta ke zugata wallahi baranma Daso. Jiya a kasuwa sun haɗu da Daso naga ta bata ƙunshin wani magani naji ana cewa da tayi amfani dashi Shikenan. Ni dai iyakar abinda naji kenan. Adda kiyi a hankali Hama hatsabibiyace" Dariya nayi ina mamakin Daso, ita da take ƴar uwata amman da ita aka haɗe kai ana son sai anga bayana. Ni zancan asiri_asirinnan na Hama zancan gaskiya yana tsoratani duk da na dogara da Allah, amman bansan wacce iriyar illa zatai mun ba a kwana a tashi. Numfashi naja nace ma Baɗɗo. Da izinin Allah asirinsu bazai yi tasiri a kaina ba. Bari in baki tea da ƙwai ki kaima Dada, kullum kafin ki fita ki leƙo ki tafi mata dashi. Itama saida taci nata ta fita dana Dada da garin tuwonnan. Suna fita na nufi ɗakin Yafendo na tsiri yi mata kwalima na gyare mata ɗaki tas na fito da wankinta na haɗe da nawa na wankesu tas. Na wanke ƙazamin bayan gidan tas da toka, na tusa sharar tsakar gidan. Sai gidan ya dawo abun sha'awa har wani fili ya sake yi gidan yana da yalwa sosai da sosai. Da rana na dafa mana farar shinkafa ina da miyata a ɗakin Yafendo naci nawa, yaran gidan duk da iyayensu suna ajjiye musu abinci a ɗaki na harhaɗa kansu na zuba musu a tire suka daka wawar abincin. Can sai gasu Yusufu da Kari sun shigo, a ɗakin Yafendo suma suka yada zango aka gaggaisa na zubo musu abincin. Kari na cin abincinne take sanar dani. "Dama Dada ce tace mu zo mu sanar miki an siyo shanun, harda tumakai biyu da akuya. Zuwa anjima Amaduyal zai kawo su nan gidan shanu sunyi kyau" Murna ta kamani sosai, Yafendo ta sanya mana albarka ta riga tasan komai a wajen yayyenta. Na tambayi Yusufu ya suke suna dai samun abinci ko? "Wallahi a'a Adda ana bamu dai na safe. Amman na dare wata rana sai dai Cubu ta siyo rogo a ɓoye ta kawo mana muci, ko ƙosai, ko ƙarago. Dama Kari ce ke sa mana abinci kafin Baffa ya koresu. Shiru nayi idona ya cika da hawaye Yafendo tace. "Yanzu su Hassana sai su hanaku abinci dan basu da imani bayan taƙamar tasu dukiyar ta Daso ce akai mata fin ƙarfi?. Babu komai ke Jabu aiki ya sameki sai ki ƙara sanwa su dinga zuwa suna ɗaukar abincin a wajenki. In yau kin basu, gobe sai Baɗɗo ta basu. Mu ba ma bari su tagayyara ba, watarana sai labari.' Godiya nayi ma Yafendo sosai, Yusufu shima yayi farin ciki sosai da wannan bayanin. Hakan kuwa akayi dan su Yusufu basu tafi ba har saida na gama abincin dare, shi ya tafi musu da nasu, Kari kuma ta tafi dana Dada bayan taci nata. Yafendo ma na miƙa mata nata. Nan na shiga hidimar tarbar miji, ina jiyo hayaniyar dawowar su Baɗɗo masu tuwon dare, sai su kai goman dare basu gama tuwo ba. Takwas dai-dai Yaya Hamma ya shigo dan naji muryarshi abun mamaki sai naga har minti talatin bashi ba dalilinshi, ni gashi naci kwalliya kuma naci alwashin saina nuna ma Hama shiru_shiru ba tsoro bane. Ai saina ɗauki mayafina na yafa na fice. Hama na kitchen nayi shigewata ɗakinta ga zahiri yana ciki ga takalmin robanshi nan a ƙofar ɗakin. Cusa kai nayi da sallamar da buɗe labulen a tare. Yana zaune babu riga daga shi sai dogon wando, ba laifi yau ɗakin ba a hargitse yake ba anyi mai gyara buja_buja. Yana riƙe da yarinya yana mata waƙa da fullanci. "Jabu irin wannan ƙyalli da kikeyi kamar wata ɗan dare sha biyu?" Wata basarakiyar murmushi nayi mishi na nemi daf dashi na zauna jikina da nashi na gugar juna, na wani narke mishi duk na sukurkutashi da kallo masu fassararo. Da shawaba nace. Naji shigowarka tun ɗazu sai naji ka shiru. Nazo na ganka a tuɓe ka manta kwananane?" Idanunshi har sun ƙanƙance, hannuna ya kama ya ɗan matse a nashi ni dashi du muka lumshe idanu na sake shigewa jikinshi. Yayi daidai da shigowar Hama da tiranta na silba. Ba shiri ta saki tiran komai ya watse ji kukeyi rakwacam. Tasha kwalliyarta harda janbaki. Atampar jikinta ta amsheta ban ɓoye muku ba Hama a fulaninma ita kyakkyawace wallahi saida gabana ya faɗi data shigo dan koni tayi mun kyau, damma dinkin yayi mugun yi mata yawa rigace a mugun ɗangale har cikinta ana gani wuyan rigar kuwa baya ko zama. Amman dake atampar ja ce sai ta haska. "Me zan gani wannan Hamma. Baka sanar mata yau kwanana bane da zata ci kwalliya ta shigo mun ɗaki sabida neman fitina. Da nice nayi haka ace ban kyauta ba. Jibi yadda ta matseka har kana riƙe hannunta sabida rashin kunya" Da fullanci take du wannan maganar, tanayi tana hawa tana sauka, dan masifa har hunhuna hancinta yake yi. "Shigowarta kenan kema kika shigo. Meye laifi danta shigo ɗakinki, da kike maganar ta zauna kusana na riƙe hannunta. Matatace halaliyata ai kin sani" ya faɗa mata haka, ai saita sake hawa tace. "Sai ku bari kuje ku karata ranar girkinta bawai ranar girkina tazo har ɗakina ta nuna mun ta fini iya kwanciyar Aure ba. In banda Hamma kana da kamata kyakkyawa wanke hannu ka taɓa me yasa ka auro Jabu oho.." "Kiyi mun shiru baki da hankaline" Ya daka mata tsawa, ni kuma nayi murmushi na miƙe. Hama gadararta kyaune, ni kuma ina gadara da ƙirar da Allah yaimun musamman mazaunaina wanda nasan yana rikita kan maza, kuma shi kanshi Hamman mazaunan suna daga cikin abinda suka fi fisgarshi game dani. Ba yabon kaiba ina hamdala da irin dirin da Allah ya bani, ko a fuskar ni ba mummuna bace, na yarda a fuska Hama ta kereni ovar, amman baya ga haka na fita kayan alatun more rayuwa sau dubun dubata. Saida na yi taku na kaɗa mazaunaina sosai kana na juyo. Yaya Hamma ina jiranka karka daɗe. Bazawara kwana uku take dashi, a iyakar sanina kwananka biyu a ɗakina. Bazan iya sarayar da kwanana ba, dan na fita buƙatar kwanan" Ina dasa aya nasa kai na fice. Wane tudu wane gangare sai ga Yaya Hamma ya biyoni. A wannan daren na wanke mishi kai tas, abubbuwa da yawa sun faru masu tsaiwa daram a zuchiyoyi, muka wayi gari cikin farin ciki da shaƙuwa a tsakankaninmu, na jefa Yaya Hamma a duniyar da nayi imanin bai santa ba kafin ni. Wannan saiya zama matattakalar ƙara buɗe sabon faifayin sona a zuchiyar Yaya Hamma, yana ji dani sosai, wallahi baya son ganina a damuwa ko ɓacin rai. Tun asuba Hama ta wayi gari da dukan yara da zaginsu a nufinta na hucewa a kansu. Ina jiyota Yafendo na mata faɗa, shima uban gayyar bayan ya gama shan soyayyarshi daya fita ina jiyoshi yana mata faɗa. Ni ko a safiyar ranarma bata ganni ba har ta gama dafa madara suka kama hanyar tallah. Bayan na gama aikin shara da wanke bayi dana ɗaurama kaina , na dafa abinci mai yawa, na kaima Yafendo nata. Yafendo zanje gida, yau nake son buɗe kayana na siyarwa. Daga nan duk zan leƙa maƙota in sanar musu" Murmushi tayi tace. "Ƴar albarka. Yi tafiyarki zan shiga da kaina duk in sanar musu zaki kuwa kwanɗa ciniki mu nan mata suna da kuɗaɗensu babu laifi. Bari mu fita tare" Abun sha'awa a tare muka fita, ni na tafi gida ita kuma ta dinga zagaye gidajen wannan gunduma tanai mun tallah. Ina isa gida na tarar da Dada da Kari a tsakar gida, Dada na kwance Kari na wanke_wanke. Ganin Dada na hutawa shine farin cikina ko iya haka burina ya gama cika sanadiyyata Ƙaddararren aurenta ya mutu, sannan sanadiyyata ta dena yawon wahalar talla itama ta soma morar haihuwa ai bata ga komai ba in sha Allah saina biya mata makka taje kafin rai yai halinshi. Muna haɗa idanu tayi mun murmushi mai kyau. Danma bata sakewa dani kundai san halin fulanin daji. Amman murmushinta shi ya nuna taji daɗin ganina. Gaga_gaga na shiga buɗe kaya na soma da buɗe zannuwan gado. Wasu ƙananan zannuwan gadone masu ɗawisu suna da santsi, na kwasosu da yawa gaskiya sabida suna da sauƙin kuɗi. Masu tsadar ɗan jejjefosu nayi. Dogayen riguna kuwa gaskiya masu kyaune giredi wan baƙaƙe sunfi yawa. Ina kam ciccira rigunan na soma jin sallamar mata Yafendo na ta tawo mun su. Allah cikin ikonshi wannan zannuwan gado sai suka tafi dasu, a ƙauyan kab su basu taɓa ganin irin wannan zannuwan gadon ba. Du mata gomannan da suka zo ganin kaya saida ko wacce ta sai ganin gado nera ɗari dubu ɗaya kuɗinsu. Dogayen rigunan kuma ɗari biyar biyar ko wacce ƙulle da gyalenta. Hayaniyar matannan ita ta jawo mun hankulan matan maƙota gida fa sai ya ɗinke da mata. Alhamdulillah zannuwan gadonnan an kwashesu duk da dogayen rigunanma an jidesu na kama ƴan ƙudaɗena na ɗaure. Wajajen azahar gidan ba kowa, bayan nayi Sallah saina zuba ma Dada abincinta na zuba nawa, wanda yayi ragowa na miƙama Kari da yaranta. Yafendo dama ko zama batai ba rako wannan mata kawai tayi ta koma ta bar yara ƙanana a gida. Zuwa bayan la'asar saina ɗau haramar komawa gida. Na bar riguna ashirin, da zannuwan gado ashirin na danƙa a hannun Kari akan in wasu matan sun shigo siyan kaya saita nuna musu. Na bata doguwar ruga biyu nata da zanin gado. Na ɗan tsinci digayen rigunan da zanin gadon na sa a leda. Naima su Dada sallama na koma gida. Abinci na ɗaura na shiga aikin shara duk da ɗakin a share yake amman so nake in ganshi ƙal_ƙal. Ina gama sharar saiga ƴan tallah sun shigo. Bayan sun nutsa na fitar musu da kaya suka kwashe, har Hama saida ta sai doguwar riga baƙa da zanin gado. Rai a turɓune ta kunce gefen zani ta ƙirgomun kuɗina na dafe. Banyi tunanin zata ko kalli kayan ba, dan dana je wajen nai musu sannu tana wanke_wanke bata ko ɗago kai ta kalleni ba. Jin yadda ake kururuta zannuwan gadonne yasa ta wanke hannunta tazo kashe ƙwarƙwatar idanunta. Da magriba Yusufu yazo ya ɗaukar musu abinci, na haɗa mishi dana Dada. Amaduyal ma da yazo ɗaure shanu saida ya shigo na cika mishi kwano da abinci ya cinye. Ni dai ina yin sallar isha nayi kwanciyata dan nasan yau Hama ba zata barshi yazo ko gaisawa mu yi ba. Ai kuwa wajajen sha ɗayan dare ina bacci naji ya faɗo ɗakin. Da sauri na farka dan tsoro ya bani ma. "Gimbiya har kinyi bacci ba tare da kin sani a idanunki ba? Ni inacan gangar jikinace acan ruhina yana tare dake" Yayi maganar yana shafa fuskata. Lumshe idanu nayi nace Nasan ƴar rigimar matarka ba barinka zata yi kazo ba, kaga shi yasa nayi baccina amman kana ƙasan zuchiyata can ciki" "To da fatan kina lafiya?" Sai alkhairi ya aikin, da fatan ka dawo Lafiya?" Murmushi yayi yace. "Lafiya lau wuni nayi ina tunaninki. Nayi kewarki sosai. Yanzu dai da safe ki shirya zan kaiku gidan ogana matarshi ta haihu gobe suna zaku je mata dan ta dameni da gori" Nan mukai sallama ya fita. Lumshe idanuna nayi bacci mai cike da mafarkai yayi sama dani. Washe gari kamar kullum na gama duk abinda ya dace da sauri dan Yaya Hamma ya turo Hama yace inna gama in samesu a ɗakinta. Kwalliyar leshi nayi fari sol mai kyau da tsada, takalmina da jakata masu ruwan zuma na ɗauko ɗankunne da sarkar gwal na saka, da awarwarona da zobunan zinare, turare mara ƙarfi na fesa a hammatata dan gudun yin warin zufa kunsan mu masu ƙiba gaskiya ba wuya munyi zufa, daga zufa sai warin hammata yanzu saimu gume waje. Shi yasa ko wankana yana ɗaukar lokaci ba laifi dan sai nayi cuɗa da ɗauraya sosai. Zanin gado ɗaya na ɗauka na sa a jakar leda ta ƴan gayu zan kaima mai jego. Tun sasssafe na aiki Amaduyal da yazo kaɗa shanu gida ya kwaso mun kaya na loda a wata babbar jaka. Fitowa nayi tsakar gidan ba kowa, sallama nayi ƙofar ɗakin Hama suka fito muka kama hanya. Babu laifi Hama tayi kyau kunsan farar mace akwai haskawa atampa koddibuwa ce mai ruwan kore da ruwan madara. Sai dai fa mayafi mai ruwan bula ta saka sai takalminta baƙi, da wata cinyayyar jakarta ja abunta. Kuma ita da gaske ta kece raini haka take ji dan taƙu ɗaiɗai take yi. Haka dai muka shiga cikin gari Yaya Hamma ya kaimu gidan oganshi anguwar masu kudi tabkeken gidan sama. Har falon gidan ya shiga damu, yasa masu aiki sukai ma Hajiyar gidan magana. Mace mai karamci da faram_faram sai gata ta fito tana walƙiya. "Ah Hamma masha Allah wannan mata zuƙa zuƙa haka ga siririya ga duma_duma. Bayin Allah sannunku da zuwa kuzo mu shiga ciki" Nan Yaya Hamma yai mana sallama akan da yamma zai zo ya ɗaukemu. Hajiyannan har uwar ɗakinta ta kaimu muka zauna a cikin ƙannenta. To kunsan mu yarbawa bamu da son jiki, saina sake na shige dangin Hajiyannan mukaita aikin girki, muka gama kuma na wanke musu wajen tas. Hama kuwa tunda ta zauna saita noƙe ta sake takurewa. Kafin a taru na ba Hajiyarnan zanin gadonnan gudunmawata, Hama kuma ta miƙa mata omo data ƙunso a jakarta, kafin Hamma ya tafi ya bamu ko wacce dubu akan ta bada gudunmawa. To tunda ko wacce na da abin bayarwa saita miƙa ta soke dubunta. Da naga taro yai taro an cika an batse saina kunce haja. Allah cikin amincewarshi wallahi kaya suka ƙare kab har ana nema saida nayi cinikin nera dubu arba'in ku kunji rabo. Wannan Hajiyarma tace in kawo mata zanin gado amman in bata sari tana da shago a kasuwa na zannuwan gado da su ledar tsakar ɗaki da kafet. Wata baiwar Allah ma tace in mata kwatancen gidana zata zo sarin riguna tana shiga ƙauyuka cin kasuwa. Na mata kwatance, gidana ta sanar dani gobe zata shigo. Haka wunin sunan ya kasance dai, akwai wata baiwar Allah ita kuma magungunan mata ta kawo, nima har na sai wani magani da naji anata yabon kyanshi. Hama ta kalleni ta kawar da kanta. Amman dana juya baya saida ta miƙa dubunnan ta kwashi kaya itama. Da yamma da Yaya Hamma yazo kwasarmu Hajiyannan ta cika mana kuloli biyu da abinci babbar kular farar shinkafa ce, ƙaramar kular kuma miyar naman saniyace a ciki, banda lemo da ruwan roba, da cincin duk saida ta haɗa mana. Mu tara gobe in Allah ya kaimu MRS BUKHARI Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 na kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (6) ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 "Sai yaushe Hamma zaka sake kawo mun Jabu zuwa na musamman? Na yaba da'ita sosai, kaga har Halima ƙanwata tace tana sonta da ƙawance naga har adireshin juna suka karɓa, ita tana aure a Girei ne" Ɗan murmushi Yaya Hamma yayi ya sauke kai. Hama ai saita haɗe fuska tai kicin_kicin. "Hajiya zan kawota duk ranar data shirya in sha Allahu" "To to Shikenan. Jabu zannuwan gadon zasu kai guda nawa wanda ya rage miki?" Ta tambayeni. To gaskiya da yawa dila guda na buɗe, sai dai ki faɗi guda nawa kike so" "Kice Hajiya ce. Ko da yake Hamma ya ba Alhaji labarinki lokacin baki dawo saudiyya ba. To a ba Hamma guda talatin ya kawo mun, zai tawo miki da kuɗin" Faɗin da Hajiya tayi Hamma ya sanarma Alhaji oganshi labarina ba ƙaramin kura Hajiya ta kwanto ma Yaya Hamma ba, dan sai kallon Hama yake yi a _ido_a_ido. Tako turɓune fuskarta, daga ƙarshe ma wajen ta bari sai a bakin get muka taddata, muka koma gida duk a gajiye, ni dai da nasan ba kwanana bane, ɗakin Yafendo na leka nai mata sannu da gida nayi shigewata ɗaki. Nasan masu jiran abincina dole suna can suna jira, dole na kunna risho na ɗaura macroni fara. Ina kan dafawa saiga me sunan Yafendo ta shigo bako sallama da roba a hannunta an shaƙo shinkafa an camɓala miyar akwai. Hancin yarinyar du majina, kayan jikinta kuwa du ƙura. Kije kuci ke da ƙannenki kinji yarinyata" Bata jin Hausa ni kuma fillancin nawa baikai yadda zan mata bayani ba. Ta dai fita da abincin ta mayar. Ina zuba ma Yusufu da yazo yanzu abincinsu dana gidan Dada sai Hama ta fado ɗakin bako sallama har tana tuntube da ƙafar Yusufu, daga ita sai ɗaurin ƙirji. "Na aiko yarinya kin dawo da'ita ina cin abinci kinsa an tasoni" Tana magana sakaka kamar goyon kakannin. Murmushi nayi nace. Na riga da nayi girki ki karama yaran suci" Saita fice fuu. Washe gari sai rigima ta kaure tsakaninta da Hamma. Ashe tunda aka kawoni aketa faman rikicin dole sai dai mu dinga yin girki ɗaya kamar yadda mijin yake ɗaya. Kunsan ƙauye suna da riƙo da al'ada, rikici har gaban Yafendo ita kuma a ƙoƙarinta na son a zauna lafiya sai tace. "Tunda dama hakan akeyi, kuma daga yau kuyi hakan banason wata magana kuma. Ke Jabu ki soma girki da abokiyar zamanki tunda girkin naki ne yau. Ke kuma ki sani akwai kwanon ƙannenta dana mahaifiyarta da ake sama abinci saiki dinga sa sanwa dasu. Banason ƙara jin wata fitina." Inaji ina gani haɗa girki ya tabbata. A ranar ansha waƙe a tsakar gida kafin su fita tallar nonon. Na shige ɗaki naci kukana na share hawayena ni bansan ta yaya zan iya ɗanɗana girkin Hama ba. Mai gayyar ya dinga rarrashina kafin ya tafi aiki. Da zai fita sai Hama sai taga mun fice tare, sai hankalinta ya tashi. Ina ganinta har ƙofar gida ta fito bata koma ba saida muka yi kwana. Ni kuma zannuwan gado na kwasa a gidan Dada na bashi zai tafi ma matar Oganshi. Na jido kaya Kari ta tayani muka kawo gida, daga haka sai muka ɓige da hira har wannan baiwar Allah mai sarin dogayen riguna ta iso. Tako sari riguna sosai ta caskemun kuɗaɗena kuma tace. "In sun ƙare gobe ma zaki iya ganina na dawo. Yola zan kai kayan gobe akwai cin kasuwa, ko mai mutum yakai ƙarewa yake yi." Nan tai mana sallama dai Gaga_gaga haka ranaku sukaita zama wata, al'amura sunata sauyawa. Tunda muka haɗa girki, duk ran girkin Hama su Dada basa samun abincin arziki. Sannan karfa ku mance ita Hama abincin dare dana safe kawai take yi da rana dole ni in ɗaura tukunya in girka, daga baya ne na dena girkawa sai dai in dama mana nono da fura musha, ni da kaina nake tatsar madarar in mayar da'ita nonon. Duk kwanan Hama abincin da take kawo mun saita bado magani a ciki. Ni dai ban taɓa ci ba, hatta banɗaki in zan shiga saina sake wankewa sai inga garin magani a kasan bayan gidan an barbaɗa mun. Har wata baƙar laya na tsinta a tsakiyar gadona, na ɗauketa da bismillah. Karambani irin nawa maimakon in cillar saina buɗe layarnan. Zanen mace na gani a jiki, an caccaka mata abu a mararta, sai gashi silli ɗaya, da ƙwayar barkono guda bakwai. A shara na cillar na ja bakina nayi shiru. Ta ɓangaren Yaya Hamma kuwa ina ganin soyayya ta haƙiƙa na fahimci ɗakina ya mayar dandalin nishaɗi da nutsuwa, dan kullum sai yayi mun waƙar soyayya. Soyayya ta yi soyayyar da duk ran asabar da lahadi ina rakashi kiwon shanu, sai in dafa mana abinci insa a wata jaka da ruwa da komai in bishi mu kutsa jeji muna tafe muna hirarmu ta soyayya. Da wannan soyayyar na jawo ra'ayinshi na askeshi tas yana noƙewa ni dai ina sara. Kunsan Allah sai da yayi zazzaɓin wannan aski da nayi mishi, wajen har kumbura yayi na kwana biyu kafin ya saɓe. Wanka kuwa Alhamdulillah yana yi, yana goge bakinshi, kayanshi na ɗakina suna samun wanki mai kyau har turare nake fesa mushi. Kayayyaki kuwa sai karɓuwa suke yi a_ hankali _a_ hankali kaya nata tafiya. Harna sake sayo Shanu, na sake siyo tunkiya inata kiwon abina, Kari kuwa ta koma tallar Nono tana girkinta ita da Dada, amman hakan baisa an dena zuba ma Dada abinci daga gidana ba, haka su Cubu. Matar ogan Yaya Hamma kuwa ya kaini naje na wuni mata, da zan dawo ta hadoni da goma sha tara na arziki. Ƙanwarta Halima naje mata itama tazo mun. Ashe layin su ɗaya da layin da Daso take aure. Gidanta yafi ko wanne gida kyau a unguwar. Dake Yaya Hamma ne ya kaini shine yake nuna mini gidan Dason. Da yamma da yazo ɗaukata sai muka ratsa bata dawo talle ba. Gaga_gaga dai anata tafiya ana ƙarawa da haƙuri da kawar da kai. A cikin matan ƙannen Hamma Safiya ce kaɗai muke shiri, duk sauran basa shiga harkata bana shiga tasu harkar, sun haɗe ma Baɗɗo kai ta dena jin daɗin zaman gidan. Ba dama tazo ɗakina ko ni in shiga nata ɗakin sai tsogumi a tunaninsu sai gulmace zata haɗamu. Dan a zauna lafiya sai nace da'ita tayi zamanta ma dinga haɗuwa a gidan Dada. Amman in na ɗan dafa abin ɗaukani ina zuba mata, harsu matan gidan ina basu kuma su lashe, amman saidai in ɗauki kwanono a bakin rijiya an yasar mun dashi. Wata ranar juma'a nice da kwana, gaga_gaga na gama aikin tuwon dare na sallami kowa, Hama na bar mata nata a kitchen dama anan nake ajjiye mata inta dawo ta ɗauka. Na shalla wanka, jiki ƙamshi ɗaki ƙamshi ina harɗe misalin tara na dare Yaya Hamma ya shigo. Me zai faru, kamar yadda na saba tarbarshi da gudu in rungumeshi haka naje, duk da yana tsantsar jin kunyar hakan amman yanaso dan bai taɓa hanani ba. Ina isa wajen sai ya ja da baya yace. "Dakata karki taɓani" Ai sai nayi dariya a tunanina ko zolayace ashe da gaske yake, saida na rungumeshi sai ya ɓanɓareni a jikinshi harda jan tsaki. Da ƙyar na juyo na zauna a gefenshi ba guiwa. Lafiya wani abun nayi, ko wani ne ya ɓata maka rai a waje?" "Ba wanda ya ɓata mun rai, dan Allah ki rabu dani banason surutu" Yana faɗar haka saiya koma kan gado yayi kwanciyarshi. Banfa daddaraba na juye ruwan wankan dana sabar mishi na kai mishi banɗaki. Yaya Hamma na kai maka ruwan wankan" Ba sai ya kawo mun mari ba, nayi maza na kauce ya mari iska. Ai sai hawaye shar_shar_shar." Sai ya shiga faɗa yana zage_zage ni bana sanin ma abinda yake cewa. Wallahi Allah ana cikin haka sai firit Hama ta shigo itace harda zama a bakin gadona. "Menene nake jiyo hayaniyarka, wani abunne?" Ai saina zama ƴar kallo suka zame mun sinima su kuma. Sai ya shiga jero mata bayani, wai daga shigowarshi na ɓata mishi rai, kuma yace in rabu dashi saida na sake yi mishi magana". Uwar kusasu ta samu abinda take so. Saita shiga rarrashinshi, kunga har ƙirjinshi take shafawa. Bantaɓa sanin haka kishi yake da zafi ba sai yau. Dan har wani duhu_duhu nake gani, ji nake kamar in dira a wuyan matsiyaciya. Sai idanu na runtse wata gobara na ruruwa a zuchiyata. Tunda na runtse idanuna inaga tun tara da rabi, bani na buɗe ba sai goma da minti goma,minti arba'in tim nayi. Wannan rufe idanun da nayi Allah kawai nake ambato dan nasan shi kaɗaine zai kawo mun agaji, har ita alkinkimar ta fita ni banma sani ba. Shiko Yaya Hamma yayi bacci abinshi harda minshari, niko ina zaune ga kayan abinci a gabana inata tubka da warwara, amman na kasa gane dalilin fishin daya zama sababin wannan tashin hankalin. A zaune a wajen bacci yayi gaba dani. Cikin dare na tashi naita adda'a ina roƙon rabbissama wati war ardi ya kawo mun ɗauki na shiga tsaka mai wuya. Ina zaune ina salatin Annabi har aka kira assalatu. Abinda yafi bani mamaki har ana niyyar shiga sallah Yaya Hamma baiko motsa ba. Abinda bai taɓa yi ba, ana kiran assatu yake miƙewa. Yaya Hamma, Yaya Hamma lokacin sallah yayi za'a shiga Masallaci " Hmm kunsan daya tashi a zabure me yace dani? Abun da ciwo cewa yayi. "Ke mahaukaciyar inace, haka a gidanku aka koya miki tashin miji marar tarbiyya" Haka fa yace mun Ita zuchiya bata da ƙashi, raina ya ɓaci idanuna sun rufe sai nace. Ni ina da tarbiyya Allah dai ya baka haƙuri naga zuchiyarka a kusa take, ko lefin me nayi oh...." Ba sai jini ba, a ina? Naushi ya kaimun a bakina, zafin ya ratsani kau. Kafin in tare naji yana dukana takota ina ya samu tsoka. Niko bakina na toshe da hannayena bibiyu ina gudun kar kishiya ta jiyo ihun ana jibgarka taji dadi. Saida ya dokeni iya iyawarshi ya fice. Saina durƙushe na saki kuka marar sauti. Idona a kumbure, guda ɗaya, dishi_dishi nake gani dashi, dan mugun naushi Yaya Hamma yaima idon. bakina na ma haka, jikina yayi laushi, gashi zuchiyata tana cikin ƙunci. Yau nice miji yasa hannu yaimun shegen duka haka? Babu komai akwai Allah" Hawayena na share, na ɗauki mayafina daya faɗi garin duka na yafa na fito hannuna ɗauke da tiran abincin jiya da daddare. Ina fitowa naga gilmawar Hama ta fice a guje daga lungunmu, nayi imani laɓe tayi mun. Ba yau bane kaɗai ba, ina zarginta sai dai yau ta tabbatar mun da zargin. Ko a zuchiyata na tuna Hama ita ta shiga ta fita tayi asirin farraƙani da Yaya Hamma. Amman sai nayi saurin tuba bisa furucina. Ba mai yi sai Allah. Hawayen daya cicciko a idona na mayar da dabara na fito tsakar gidan gabana na faɗuwa. Sai nake jin inama ƙasa ta tsage in faɗa da wannan abun kunya. Aiko da Hama na soma cin karo ta kafa ta tsare. Banko bi ta kanta ba, na dai jiyo tana waƙar fulani. Ni dai ta kaina nake yi, wani irin mugun sarawa kaina yakeyi, idona inaji kamar zai zazzago. Ina hura wuta Baɗɗo ta shigo. Tana kallona ta riƙe mun hannu. Sai hawaye shar_shar a idanunta. Cikin jarumta nace. Ki dena kuka babu komai Baɗɗo. Bari in gama dumamennan ki sameni a bayan layi sai muyi magana." Tukunyar tuwon dana yayyanka na ɗaura, ɗaya gefen na ɗaura miyar. To ni a gaskiya inna ɗaura abinci a wuta bana ko motsawa ina zaune har saina raba. Dan gudun kar a cutar dani, irin magungunan da Hama take sassakamun yayi yawa. Saida na raba dumamen matan gida suka soma shigowa. Da suka ga yadda halittata ta sauya, sai wannan ta kalli wannan, wannan ta kalli waccan. Haka kuma ina jiyota da Yaya Hamma a tsakar gida sai dariya takeyi. Ni dai na gama abinda zanyi na ɗakko namu abincin na fito. Amman me Yaya Hamma harya fice abunshi. Na gyaɗa kai tare da haɗiye yawu mai ciwo. Koda na shiga saina sau kuka kawai. Ina cikin rera kukannan sai ga Baɗɗo da Amaduyal a guje sun shigo" "Adda Adda shanu sunata mutuwa kizo ki gani" A guje ni dasu muka fita. Allahu Akbar lallai an sabautani dan duk manyan shanun sun faɗi sun mutu sai kumfa ke fita a bakunansu da halama wata gubar aka saka musu. Ragowar ƴan madaidaitan da basu ƙarasa mutuwa ba Amaduyal yasa kansu gabas ya yanke. Matan gida dana maƙota duk suka cika gidan tam anata tayani jaje, ga gulmar ganin bakina da idanuna da suke ta tayi. Ana cikin haka saiga Yafendo ta kutso ta iso. Ga shanaye a kwance riɗa_riɗa sun mutu shanaye masu tsada ƙosassu. "Ko wani abun suka ci a wajen kiwo Amaduyal? Wannan lamarin da girma yake, shanu manya haka? Maza je ka kirawo Baffanku" Da sauri Amaduyal ya fita, Yafendo tana kalloni taga a halin da nake. Sai ta dafani" "Jabu me ya samu idanki duk ya kaɗe jini ya taru, ga bakinki a fashe?" Munafurci irinna matan ƙauye duk sai su kayi tsit suna jiran amsata. Faduwa nayi a banɗaki na taka sabulu" Hama najin haka ta saki murmushin da karaf a idona tayi wucewarta. Hannuna Yafendo ta ja izuwa ɗakinta ta zaunar dani a gado. "Kuna faɗa da wannan yaron ne Jabu, ki sanar dani gaskiya dan ina lure da abinda yake faruwa a gidan. Bana son in yi managane dan kar aka dan ku yaran yata ne ina tare muku. Hamma ne ya bigeki?" Hawaye ya zubo mun shar_shar ga raɗaɗin jiki, ga raɗaɗin zuchiya, ga raɗaɗin abinda ya faru da dabbobina nayi asarar dukiya mai yawa. Amman nayi tawakkali ina fatan Allah yasa wata musibace da zata sauka a kaina ta sauka a kan dabbobin. E Yafendo shi ya dakeni" Salati ta soma tana tattafa hannayenta. "Wannan yaron ne ya dokeki, yaushe ya zama lusari ni ban sani ba, a kanki dukan zai soma? Nasan wannan baya rasa nasaba da Hama nayi imanin tana da sa hannu akan wannan dukan, da mutuwar shanunnan naki. Bafa komai bane face baƙin ciki. Abinda dai nake so dake shine kiyi haƙuri kinji am? Ki zama mace mai juriya da ɓoye sirrinta. Hamma wankine, kuma nasan yana matuƙar sonki fiye da Hama. Itama kuma tasan haka ba zata barki ki zauna lafiya ba. Jabu kishi da fulatanar daji ba sauƙi. Da zan baki labarin irin wahalar da mahaifiyarki da Ai'i Yafendonku suka sha a hannun kishiya da zukatanku sai sun fashe. Ki duba irin yadda su Yusufu suke a ɗofane su da gidan ubansu duk sabida sharrin kishiya. Mai Nagge yaso Daso sosai mu munfi kyautata zaton asiri kishiyarta tayi ta farraƙa tsakaninsu, inaga irin asirin da Hama tayi a tsakaninki da wannan yaron kenan tunda har wannan yaron ya iya cire hannu ya dokeki." Fasali ta ja. Ni kuma tuni ƙwaƙwalwata ta lula tunanin kenan nima haka zan rayu irin rayuwar da Dada tayi a gidan mai nagge, yarana suma haka zasu kasance kamar yadda su Yusufu suke kenan, ciwon zuchiya da hawan jinine zai yi ajalina daga ƙarshe, koma Hama ce zata kasheni ta huta? Ya Allah ga baiwarka bata da kowa bata da komai. Allah kaine gatana ya Allah ka karkato mun da hankalin mijina ya dawo zuwa gareni muci gaba da shimfiɗa rayuwa kyakkyawa mai albarka. Maganar Yafendo ce ya dawo dani cikin hankalina. "Amman mai haƙuri shi ke dafa dutse har yasha romonshi. Na haɗaki da Allah kar neman mafita ko tudun dafawa ya kaiki ga bin malaman tsubbu Jabu. Ki dogara da Allah, zan dage in tayaki da adda'a. Bana son wannan maganar dukan da canjin Hamma ya je kunnen Adda Daso. Itama Baɗɗo da Amaduyal zan ja kunnensu." Muna cikin haka sai ga Baffa Musa ya shigo duk a ruɗe. Ɗankwalin kaina nayi maza na cire saina yafa kamar mayafi na rufe fuskata. Shi yama ɗauka kuka nake yi sai ya shiga rarrashina. "Tashi jeki Jabu" Cewar Yafendo. A hankali na fice na koma ɗakina, daɓas na shirgu a kujera saida ta yi ƙara tsabar ƙiba. Tunani na shiga yi. Kaddarata ta wannan karon ta muguwar kishiyace, jahilar kishiyar da ko alwala ba daidai take yi ba. Na tsallake siraɗin uwar miji da ƙyar, na sake faɗowa tarkon kishiya. Idanuna da nake ji kamar zasu faɗi na lumshe wasu hawaye masu zafi suka zubo, ina tuno sanda Yaya Hamma ya dunƙule hannu ya naushi idona, wanda hawayen daya tarwatse a cikin idon ni na ɗauke tsiyayewa idanun ma yayi. Tun ina jiyo hayaniyar matan gidan har na dena jiyosu, Baɗɗo dai yau bata je tallenba ɗan uwa abun wuya. Ita taimun duk aikina hatta abincin rana ita ta dafa mun ta raba, jikina ko ina ciwo yake yi, ciwon bayan dana kwaso a bautar gidan larabawa shima ya tashi sosai bayan har tururi yake yi mini. Zuwa yamma lis Amaduyal ya kawo mun kuɗin shanun daya yanka an siyar. Na buɗe adaka na ɗebo kuɗi masu yawa. Ka riƙe ka ba Baffa Musa a hannunshi a siyo wasu shanun. Ka ɗauresu a gida kawai a hakan. Wannan ragunan da kajin ka kaɗasu ka mayar dasu gida" Shiru Amaduyal yayi da kuɗaɗe a hannunshi yayi jimm "Adda wannan kuɗin ba kuɗin da kike juya kasuwanci bane, kuma naga kayan sun ƙare anata nema. In aka siyo shanun ke da wanne kuɗin zaki juya?" Murmushi nayi mishi. Babu komai akwai ragowar kuɗaɗe a hannuna. Uwani zata cikace mun zan saro kaya kar ka damu, a soma kashe wannan wutar tukunna" Kai ya gyaɗa kawai, har zaice wani abun sai kuma ya fasa, abincin Dada na bashi ya kai mata. Na koma na kwanta Baɗɗo kuma na sallar la'asar ina kallon abun mamaki dan ba daidai take yin Allah ba. Baɗɗo ba daidai kike sallah ba subhanallaah. Ki shirya da zaran na warke dake da su Cubu zan kafa muku makarantar dare zan koyar daku ɗan iya abinda na sani game da addini, kuma mu dinga karatun Qur'ani" Jikinta a mace mutus ta amsani da to. Ita tayi girkin dare ta raba ta fitar dana kowa, hatta ruwan wanka ita ta kaimun jiki yaƙi daɗi. Ina zaune na gama kai kukana ga Allah sai na jiyo sallamar Yaya Hamma. Ba shiri na miƙe tsaye ina mishi sannu da zuwa, banza yayi mun ya nemi waje ya zauna. Ina wuni barka da dawowa Yaya Hamma" Na durƙusa har ƙasa da ƙyar gani dama ba kaɗan ba. Hanci naga ya toshe naci wani ciwo a zuchiyata. "Jabu ɓera ne ya mutu a ɗakinne?' Yayi maganar da zafi. A'a wari ɗakin yake yi ne?" Na bashi amsa a taƙaice tare da mikewa na zauna a gefenshi. Kamar na soka mishi allura a takashinshi haka ya miƙe tsaye yana matsawa baya harya fita daga ɗakin. "Bazan iya zama a cikin wannan warin ba. Kema kije ɗakin Dada ki kwanta gobe ki duba abinda yake warin" Labulen ɗakin ya saki, sai naji kamar zuchiyata ta rushe dan bala'i. Kwanana ya miƙa ma Hama inaji ina gani. Kishi zai yi ajalina, duk da a cikin fishi da taka tsantsan nake dashi, amman duk bala'i gara ya zauna a ɗakin, ni na gwammaci ya kuma dukana daya kai kwanana ɗakin kishiya taga wallena. Baza ku gane ba nasan, wannan kishin da jiin zafin ya shafi mai kishiyane kaɗai, da waɗanda suke cikin takalmana ma'ana da matan da aka taɓa yima fin ƙarfin kwana suna ji suna gani. Tuttura tuwon da Baɗɗo tayi na dingayi na danne tuwon da madarar shanu, na haɗiyi fanado dama ina dashi da rana ma na haɗiya sanda Baɗɗo ta damamun fura. Duk ciwon da nake ji, da ƙagewar da bayana yake yi, a wannan daren saida na hautsine ɗakinnan na birkitashi. Illahirin ɗakin banga komai ba, ni ƙamshi ma nake ji a ɗakin dan ni ma'abociyar ta'amali da turarukane mada'in ƙasashe daban_daban. Duk iya bincikena dana binciko banga komai ba. Na kwanta ina nishi gami da tunanin to me ke faruwa kenan, ko dai tsabar Yaya Hamma yana son tozartanine yasa ya tsiro da zancan warinnan? Ni dai kwana nayi cur ina tubkewa in warware abuna, abin duniya yabi ya dameni ga idanu ya matsamun lamba abinda yafi komai tayar mun da hankali shine kafin gari ya waye ba sai idona me ciwon naga kamar ya dena gani ba? Sai insa hannu in doɗe mai lafiyar, shi marar lafiyan kuma yana buɗe sai duhu da ɗan ƙyallin tocila kaɗan nake gani Innalillahiwa'innailaihilrajiun na dinga ambatawa. Tada kabbarar Sallah nayi ina sallah ina hawaye ga wata ƙaddara kuma ta kuma samuna. Washegari A gurguje na sake kayan jikina, na buɗe adaka na ciro kuɗi na cusa a jaka na fito. Hama na ƙofar ɗakinta tana kwashe Manshanun data gama burgawa yanzu na iso. Baddo ma na ƙofar ɗakinta tana aikin burga. Hama dan Allah inaso kiyi mun magana da Yaya Hamma ne?" "Dan jaraba da wannan duku_dukun zaki zo neman min miji. To baya nan bai shigo gidan ba" Kafin in ja numfashi in saki sai gashi ya iso inda muke. Yana isowa ya toshe hancinshi yana ƙoƙarin shigewa ciki. Dan Allah inaso zanje asibiti Yaya Hamma" "Sai kin dawo" Ya bani amsa a taƙaice. Hama na kalla, na kuma kallonta da kyau nace. In kinfi ƙarfina baki fi ƙarfin Allah ba. Baddo yima Yuguda magana zaki rakani asibiti" Hama ta cokaro ɗaurinta gaba bata ce dani komai ba. Baddo ta bar abinda take yi ta shiga ɗaki, bata jima ba ta fito goye da diyarta. Ɗakin Yafendo muka je na sanar mata abinda ake ciki. Nera dubu biyu ta miƙo mun. "Ungo ku riƙe a hannunku, Allah ya ƙara sauƙi bazan hanaki zuwa asibitiba a birni kika rayu shiyasa, amman babu irin maganin da babu a gargajiya. Nima zan fita da hantsi inje in karɓo miki maganin idon, da tofi" Kudin Baɗɗo ta karɓa mu ka yi mata Sallama. Baɗɗo kina jin wari a jikina dan Allah?" Hawayen daya zubo mata sanadin tambayar dana yi mata ta share. "A'a Adda. Ina tunanin asirin warin jaɓa Hama tayi miki dan ta rabaki da mijinki. Jiya muna tsakar gida muna hira ai ya baro ɗakinki yazo ɗakinta. Shine take tambayarshi me yazo yi ai ba kwananta bane. Shi kuma buɗar bakinshi yace warin jaɓa kike yi mishi, dake da ɗakin. Shine nake tunanin irin asirin da Lanti tayi ma kishiyarta kenan, ita kam baiwar Allahn mutuwa ma tayi daga ƙarshe. Sai da mijin ya shekara biyu tim baya shiga ɗakinta, baya cin abincinta, baya ko kallon inda take. Wannan baƙin ciki shi yai sanadinta. Ƙaƙa sara ƙaƙa kundai ji halin da Jabu Iyabo take ciki. Ina mai ba masoya wannan littafin haƙuri domin ba zaku jini ba kwana biyu ciwon idanu ya matsamun lamba, gashi bani da lafiya ma duk ni kaɗai na yauma dauriyace kawai. Kuy mun haƙuri da zaran na warware zaku jini in sha Allah. Masu promo kui ma Anty Zee magana. Waɗanda ba ƴan kano bane akwai number wayoyinku a jikin kayan za'akai muku tasha in sha Allah. Nagode sosai sai kun jini. Ƴan nijar da mutan Saudiyya ina godiya sosai. MRS BUKHARI *Assalamu alaikum* Barkanmu da safiya, naga saƙwanninku na adda'a nayi farin ciki, naga tarin masoya kuma mabiya. Alhamdulillah idon da sauƙi zanci gaba da lallaɓawa amman ba lallai bane in dinga yi kullum ba ayi haƙuri da hakan Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (7) Maraɗi. Gwadabe:. Dariya yayi ma Hadiza ya kalleta yace. "Hadiza duniya, fitinarki yawa, kin iya tada zaune tsaye. Ayi magana kice anci miki fuska." Haɗe rai tayi tace. "Wai ni kam tsohuwar matarnan taka dame tafi sauran matane, da har yanzu ka kasa daidaita sonta da namu? Ƙila ma ta mance dakai ita sam a rayuwarta tana tare da mijinta ya kankare ka a zuchiyarta da ƙwaƙwalwarta" Haɗe rai yayi ƴar fara'ar da yake take ta tsaya. Dama tayi ne dan ta kunna mishi wutar kishi, ko babu komai ranta sai yayi fes. Washe gari Gwadabe ya bata kudi ta shiga kasuwa tayo ma ƴan takai tsaraba, har turamen atampa ya bata ta siyo mishi, da kayan yara na yaran Bara'u, da yaran Tamu. Baba Fhatsima itama ta haɗa musu nata tsarabar, ɗan kayan kwance Anti Badi'a ta tarkata tace a kaima Sakina. Malam da daddare yasa akai mishi kiran Gwadabe ya sameshi a turakarshi dashi da matanshi duka anata shari'a Sabitu ya daki matarshi har tayi yaji. Shigowarshi yasa Malam sallamar kowa sai Baba Fhatsima da take dashi ranar. "Gwadabe naji a bakin Gyatumarku kunason zuwa Takai ko?" "E Malam gobe in Allah ya kaimu zamu tafi harna yankar mana tikiti." Malam yayi jim. "Toh Gwadabe bazan hanaka shiga Takai ba ko dan Bara'u da matarshi su kaɗai sun isa ayi tattaki akai musu ziyara. Amman akwai abinda na ɓoye maka. Ga Fhatsima ita tasan komai Jamilu da yayi mun rakiya shima yasan komai. Babala tace Allah ya isanta nononta daka sha in har ka shigo Takai ka shiga gidannan. Sannan ta yanke halaƙarka da ƴan uwanka Allah ya isanta in ka je musu gida. Babu abinda bata faɗa ba. Dan haka sai ka guje ma Allah ya isanta kar ka kuskura ka shiga cikin gidanku. Hadiza da Shafa zasu iya shiga su nuna mata yara in Allah ya bata ikon ganinsu to, in suma ta korosu sai a haɗu duk ayi haƙuri. Iyatu da Hambali ke zuga uwarku akanka nayi iya tunani da hangen nesa namu na manya mahaifiyarku tana da son abin duniya, shi yasa take ɗaukar duk maganganun da Hambali ya ɗaurata akai. Da ace Allah zai ɗaga darajarka a duniya ka samu arziki zaka sha mamakin yadda komai zai wuce kamar bai faru ba. Gwadabe ka daɗa haƙuri kaji ko?" Kan Gwadabe ya ɗaure, amman baiyi mamaki ba. Murmushi yayi ma Malam kawai yace babu komai ya gode, kuma zai kiyaye in sha Allah zaiyi yadda take so ɗin. Washe gari asubar fari motarsu ta ɗaga sai Kano. Tafiya mabudin ilimi sun fito shiddan asuba basu suka shiga Kano ba sai shidda na yamma. Gwadabe na sauke ƙafarki a garin Kano yanayinshi gabaki ɗaya saiya canja, tunaninshi ya sauya, yana hasko irin rayuwar da suka gudanar shi da IYABO a garin Kano. Har Hadiza ta soma zargi kunsan bakinta baya haila cewa dashi tayi. "Hala tunanin tsohuwar matarnan taka kake yi. Naga duk ka sauya?" Baiko kalleta ba ya soma nema musu motar da zata shiga Takai. Sun ko taki sa'a motar akwai wajen mutum ɗaya daga ita kuma mota ba zata sake barin tashar ba sai gobe. A haka suka shiga Gwadabe ya zauna a injin shi. Wajajen tara da ɗoriya sai gasu a Takai abuka da ƙauye garin a cike yake dam da matasa gungu_gungu, da magidanta a ƙofar gida wasu na hira wasu rediyo suke saurare, ga yara ratata a waje sunata wasansu cikin kwanciyar hankali. Suna tafe zuwa gidan Bara'u da kici_kicin kayansu suka zo wucewa daidai ƙofar gidansu. Gabanshi ya yanke ya faɗi ras. Yau shine zai wuce gidan da aka haifeshi yayi rarrafe da wasan kasa a cikinshi, gidan da a ciki aka birne mahaifarsa. Wasu siraran hawayene suka gangaro mishi ya wuce gidan da sauri. Hadiza dai sai jejjefa kafarta take yi, babu wuta garin yayi duɗum dashi. Gaba da gidansu kaɗan anan majalisar abokan gwadabe take abokai irin na wasan kasa. Ai kuwa ilai Bara'u na wajen anata fafata musun da suka saba. "Sannunku sarakan musun tsiya" Cewar Gwadabe, da fara'arshi dan ganin tsoffin abokanshi. Nan suka soma sowa da hargowar murna. Bara'u yace. "Hadiza barka da shigowa Takai ta kawo ta saba da saukar baƙi." Murmushi tayi aka gaggaisa. Gwadabe ya gabatar da'ita ga abokanshi. Suka sake gaisawa da'ita. "To bari mu karasa inna ajjiyeta zan fito muyi hirar yaushe gamo." Ila yace. "Akwai babban labarin abokinku kai da Bara'u Zilƙifulu." Baki Gwadabe ya buɗe yace. "Zilƙi fa kace, ya dawo daga yawon duniyar kenan? Shegen kaya bari in fito gaskiya a darennan ma ni sai naga Zilƙi" Bara'u ya tayashi ɗaukar kayan shi da Ila, Ila iyakarshi dai zaure. Sakina da yara suna tsakar gida zafi kamar zai kashesu suka jiyo sallamar baƙi. Suna shigowa Sakina ta riƙe baki. "Ah_a_a_a manyan baƙi mutanen nijar. Hadiza maraba lale. Gaskiya Bara'u muna da manyan baƙi yau" Sakina tayi maza ta kunto Ummi daga bayan Hadiza. "Ga tabarma Hadiza zauna dan ɗakin baya shuguwa, kun shigo lokacin zafi sai sanƙarau aketa yi da kwalara." Zazzaunawa suka yi, nan aka shiga gaisuwa yaran kuma duk suka ruƙunƙume Gwadabe suna ga Baba ga Baba. "Shafa anan gidan ta wuni yau cur. Abba yayi wayau sosai, danma ƙurajen zafi duk sun fesuo musu har uwar wallahi" Cewar Bara'u. Ita kuwa Sakina tana kitchen taje hado abinci, Ummi tana hannun Bara'u" "Sakina ki bar tuwonki. Bari inje wajen Nalanjin in karɓo musu gashasshiyar zabuwa suci su more" Da dariya Sakina ta fito "Kaga Shinkaface da miya yau muka dafa ba tuwo ba sabida Shafa." Bara'u yayi Dariya yace. "Kice yau Toye ya cika cikinshi har ya gaji?" Itama dariya tayi tace. "Ɗan jakar uba ba. Gwadabe Toye baya son tuwon masara sam yaronnan. Dana zubo tuwo sai ya kama kuka harda birgima fa" Dariya suka fashe dashi. Gwadabe yayi ma Toye yarbanci, kafin yace da Sakina. "Dake bamu fiye yin tuwon masaraba sai Amala, ko sakwara, ko tuwon farin albo shiyasa bai saba da tuwon masarar ba" . Bara'u yace. "Allah sarki tsuntsun soyayya. Ni ko Gwadabe kana jin labarin Iyabo kuwa? Ya kamata ko ba komai ayi zumunci bai kamata muyi fatali da Iyabo ba baiwar Allah guda da bari." A_ido_a_ido Gwadabe ya kalli Hadiza, saida ta kasa jurewa ta sauya fuska. Sakina tace. "Ko da suka shigo cikin gidannan sai da Iyabon ta fado mun. Ban dakko zancan bane sabida kar Hadiza taji babu daɗi" "Hakane kuma uwargida a gafarcemu, ai yanzu kambun sarautar a hannunki yake. Gwadabe tawo muje mu siyo mata gashasshiyar zabuwa" Ficewa suka yi nan suka bar Hadiza da dariyar yake ta ciki na ciki. GWADABE "Gwadabe Yaya Hambali ya zama babban mai kuɗi, yana ɗaya daga cikin manyan masu kuɗinmu na Takai. Da azuminnan daya wuce, yayi rabon abinci na ban mamaki. Sunje sun sauke farali har su Fodiyo ya biyama. Kai kaga inya shigo Takai yadda ƙofar gidanku yake cika kuwa? Hmm abun ba'a cewa komai. Babala kuwa tana dai shigowa Takai duk wata tayi sati guda ta koma Kano. Hambali ya ɗauketa kacokan daga Takai, kuma kasan Hambali ya auri Laila kuwa?" Gwadabe da bakinshi yake buɗe dan mamaki, ai saiya sake buɗe bakinshi. "Ya auri Laila fa kace, ita auren nata kuma mutuwa yayi ne?" "Mutuwa kai. Laila ai a kotu ma alƙali ya raba auren. Gagarumar sata taima mijin na akwatin kuɗi guda. Taita facaka da dukiyarshi shi bai sani ba, lokacin fa Laila ta shigo gari. To su Yaya Hambali ne suka tsaya mata lokacin ana kes ɗin, duk zaman kotun bai wuce ni ba. To bayan Yaya Hambali ya biya shi mijin kuɗin da Lailan ta sace, sai suka nemi a raba auren kawai. To kai kasan Baba Iyatu idonta idon kuɗi nan taita naci da kuke kuken dole a cikin yaran Babala a samu ɗaya ya auri Laila ko dan a rufa mata asiri. Shine Hambali ya daki ƙirji ya aureta. Kai kaga bikin da muka sha a ƙauyannan? Ba'a taɓa yin biki irin nasu ba ni dai a iya tasowata" Kai Gwadabe yaita jijjigawa har suka siyo zabuwa suka juyo, Gwadabe ya kasa cewa komai dan mamakin abubbuwan, da mamakin yadda ya zam bare a cikin ƴan uwanshi cikin ummanshi. "Kaji labarin Zilƙi a wajen Ila ko?" Ajjiyar zuchiya ya sauke, Bara'u ya lura Gwadabe ya lula duniyar tunanin yadda dangi sukai watsin ruwan tsarki dashi, shi yasa ya kawar mai da tunani da zancan Zilƙi. "Wai ashe Zilƙi zai dawo ƙauyannan? Nifa na ɗauka ya manta da kowa" Dariya Bara'u yayi yace. "Sai gashi ya dawo abinshi. Kuma kasan abin mamakin? Shine charman na nan Takai. siyasa ya faɗa ka'in da na'in kasan Charman ɗinmu daya sauka na nan Takai abokinshi ne, shima dake saida shima ya je ya gama yawon duniyarshi ya dawo ya faɗa siyasa. To wallahi shi ya tsaya ma Zilƙi akaita shige da fice, dani akaita yawon kanfen waje_ waje har dai Allah ya karɓa mishi ya zama Charman" Dariya da mamaki Gwadabe yayi ya buɗe baki yana murna. "Charman Zulƙin? Iko sai Allah, Allah mai yin yadda yaso da bawa. Gobe zaka kaini gidanshi an daɗe ba'a haɗuba." "Ai kuwa shima sai tambayarka yake yi tun ma ana kan gangar siyasar. Kaci sa'a jiya ya dawo daga Abuja yaje taron wani semina. Gobe da sassafe zamu dirar mishi mu karya a tabkeken falonshi. Dariya du su biyun suka yi. "Ya batun nomar bana Bara'u?" "Asara kawai Gwadabe, Takai wannan karon anyi asarar dukiya noman bana babu yabanya me kyau sai dai godiyar Allah musamman mu masu noman gyaɗa har ɗan dama dama masu noman maiwa. Ya taka sana'ar maganin ka ce mun dai ka soma zuwa cin kasuwar ƙauyuka ya yanayin kasuwar to?" Sai da Gwadabe ya jajanta ma Bara'u kafin yace. "Kasuwa Bara'u babu abinda zance sai hamdala wallahi. Duk kasuwar ƙauyan dana ziyarta dana baza magani na soma yehuwa zaka ga an lulluɓeni. Bara'u fatana shine Allah ya bar abokarmu har yaranmu su gajeta. Ɗazu kayi maganar Iyabo, tunda muka rabu ban sake sa Iyabo a idanuna ba gaskiya. Amman in sha Allah inna shiga Kano ko a tasha ne zan ajjiyesu in nemi gidan Uwani. Ko kuma in barsu a nan Takai ka rakani mu nemi Uwani inji labarin Iyabo. Ko gidan naje mutuncina zasu ci har gaban abada ƴan uwanta ba zasu ƙaunaceni ba" Bara'u yayi murmushi yace. "Baiwar Allah mai wuyar wucewa. Muma muka kasa mance halacci da Alkhairan Iyabo balle kai da dominka muka santa. Abinda za'ayi shine in ka huta zamu shiga mu nemo duk inda Uwani Tabalbalin take muji labarin Iyabo, mu ajjiye mata saƙon gaisuwa. Zancan abota Gwadabe tunda zamu haɗa yaranmu aure ai zumunci zai ɗore, fatana Allah yasa kar silar auren zumuncin namu ya samu tangarɗa." Haka dai hirar wannan abokai ko Aminai yaƙi ƙarewa, gida suka shiga suka kai musu naman da suka siyo Hadiza da Sakina sai hirarsu suke gwanin sha'awa. Su kuma suka ɗauki abincinsu suka fita dashi waje yara suka kawo musu tabarma da fululluka dan a ƙwar gidan zasu kwana. Washe gari. Da safe Gwadabe yasa Hadiza ta cicciro tsarabobin da yayi ya cire na Sakina da yara, ya cire na Bara'u. Na gidansu Shafa ma ya cire ya ajjiye a gefe. "Wannan in Sakina zata kaiki gidansu Shafa sai ki tafi musu dashi ko, wannan kuma na gidanmu ne" "Dama nice zanje ni da nazo garinsu? Aina ɗauka itace zata zo ko?" Ƙur yayi mata da'idanu su biyu ne a ɗakin ta gamama Ummi wanka kenan tana mata nabkin. "Kiyi abinda nace miki a matsayina na mijinki. In kuma ban isaba to sai ki zauna. Kar Sakina ta kaiki gidanmu tukunna dan su Babala basa nan." Baki ta zunɓuro tace. "Amman ai ita....." "Ya'isa haka Hadiza. In baki bi umarnina ba zan saɓa miki mai taurin kan tsiya marar jin magana baki da aiki sai ƙorafi mtwssa Yaja tsaki ya miƙe ya fice. "Gwadabe munga tsaraba fa Allah yasa a mizani, Allah ya bar zumunci" "Sakina kenan baki da dama. Bara'u muje ko?" Bara'u yace. "To muje. Sakina gidan Zulƙi zan kai Gwadabe yaushe rabon da'a gana" "Allah sarki, sai kun dawo kwa gaishesu. Muma da mun kammala zan zazzagaya da Hadiza duk gidan daya dace dai. Gida kuma Babala bata nan inta dawo wannan aikin naka ne banma isa na kai Hadiza wajen Babala ba" Da haka sukai sallama zuwa gidan Zulƙi. A harabar tabkeken gidan nashi suka zauna a wasu fararen kujeru me gadi ya shiga sanar mishi da zuwan na Bara'u. Bara'u ba baƙon gidan bane an saba ganinshi hatta ƴan sandan dake tsare lafiyar Zulƙi sun sanshi. "Rigiji gabji lallai Zulƙi yafa samu duniya ji gida ma malam, ji ma'aikata da masu tsaro, ga motoci har uku." "Bafa kaga komai ba Gwadabe bari dai mu shiga cikin falon ka gani" Me gadine ya ƙaraso inda suke yace. "Hajiyar gidan tace a muku iso zuwa falonshi. Bacci ya tashi yanzu wanka yake yi zai zo ya sameku inya fito" Tiryan_tiryan suka bishi har zuwa masauƙin baƙinshi inda anan yake zantawa da baƙinshi irin masu unguwa, mai gari, da hakimai, da dakatai" Masu aikin girki suka kawo kulolin abinci da filas na shan shayi da kofuna. Gwadabe sai karema falon kallo yake yi. Yana mamakin wai wannan gidan na Zulƙi ne" zamansu baifi da minti talatinba sai gashi ya shigo yana saye da shadda wagambari ɗinkin tazarce. Baki ya buɗe ya nuna Gwadabe da yatsanshi yace. "Gwadabe yau kaine a gidana, to yaushe ma ka shigo garin?" Da sauri Gwadabe ya miƙe suka tafa da Zulƙi suna dariya gami da farin cikin ganin juna yaushe gamo. "Ranka shi daɗe ashe rai kanga rai?" Zulƙi yayi dariya suka zazzauna yace. "Bara'u kaji ɗan iska waini yake kira da ranka shidaɗe. Ni Gwadabe kaida kake tare mun faɗa nine ranka ya daɗen?" Dariya suka saka Bara'u yace. "Ai Zulƙi ba zaka canja ba. Wai kai baka mantuwane dan Allah?" "Ba komai ake mancewa ba Bara'u. Gwadabe ai mutumne harda ɓari kai ka sani da sauran abokanmu da muka taso tare. Gwadabe wanne aiki kake yi? Bara'u dai ya tsokatamun matanka biyu kuna zaune a nijar gidan Baba Magaji wan Babala" Gwadabe yace. "Hakane matana biyu. Sana'a anata buga_buga inayin haƙon zinare. Ina tallar magungunan karfin maza na gargajiya dana bature. Kaga irinsu" Gwadabe yasa hannu a ajjihu ya ɗauko wani ƙullin magani guda biyu, dana bature sacet ɗaya. Baki Zulƙi ya buɗe yace. "Kusun uwa tafi da gidanka kenan. Gwadabe kaine ka zama mai siyar da maganin maza?" Sunfi minti koma sunata ƙyalƙyala dariya kamar waɗanda suka ga wawan zama. Gwadabe yace. "Wannan in ka zuba a tuwo kaci yajinnan Zulƙi ko kakai shekara saba'in saika dawo ɗanyen jini a wannan ranar, da miyar yauƙi ake ci. Wannan kuma na baturene shayin maza ne. Ka juye a kofin shayinka ka shanye ranar ba'a magana. Gana dattin mara, amman shi yana sa gudawa sassafe kafin aci komai ake dafawa a shanye da tuƙarshi. Ka jarraba amfani dashi zaka samomun kostoma" Bil haƙƙi Gwadabe yake musu bayani. Su kuma sai kwashewa da dariya suke yi. "Ikon Allah kenan. Gwadabe zan jarraba in naga kyanshi niko zan haɗaka da manyan mutane" "Yauwa ni dama abinda nake son ji kenan. Ya batun iyali Zulƙi, kuma wai ina katafi yawon duniya ne?" "Iyali sunanan an tara. Na jima da yin aure yaranmu shida da matar dana aura a bariki ƴar garin bayalsa ce, tana da yare. Sai bayan na hau kujerar mulki saina auri yarinyar ƙanwar Babarmu, sun matsa ni bama sonta nake yi ba, dan Jenifa ta taimakeni sosai a rayuwa. Can Bayalsa na yada zango. Dakone kwasar shara, kwata. Gwadabe babu sana'ar da bamba har Allah yasa na auri Jenifa to mahaifinta ɗan siyasane babba. A wajenshi na koyi harkar siyasa shi ya wanke mun kai yace ai zan iya komawa ƙauyanmu in shiga takarar chiyaman tunda ina da takaddar gama sakandare. Shine ƙashin bayana, Rabo kuma chiyaman daya sauka saiya tsayar dani na zama ɗan jam'iyyarsu kaji abu kamar wasa ko?" Kai duk sukaita jijjigawa, dan shima Bara'u yaune yake jin wannan labari" Gwadabe yace. "Yaya kake fama da Jama'a amma?" Sakkowa yayi yace. "A zuba abinci muna ci ina baku labarin wahalar dake cikin kujerar mulki." Dariya su ka yi. Sunsan Zulƙi tun yana yaro da zaran rana ta take lokacin cin abinci yayi ake nemanshi a rasa. Bara'u ya bude kular abincin ya juye masar dake ciki dukka a faranti, ya kwarara miyar masar akan masar ya yaryaɗa musu man shanu isasahe. Duk yayi muku komai suka tsoma hannu, saida Zulƙi ya kai noma biyar kyawawa kana yace. "Kujerar mulki bata da daɗi Gwadabe sam. Hakkin al'ummar yankunku akanka kai shugaba ya rataya. Kowa jira yake kahau ya kawo maka buƙatarshi, kuma fa dole yake nufin wannan buƙatar ka biya mishi. Yanzu tafiyar da nayi akan yadda za'a samun hannu a takaddar tallafama manoma da taki ne. Satina fin nawa ina sunturi, masu ruwa da tsakin sunƙi sa hannun." Ya dinga basu labaran yadda abubbuwan suke tafiya, da yadda haƙiƙanin siyasa take. Sunfa jima suna hira a wannan gida basu ankara ba suka soma jiyo kiran sallar azahar. A banɗakin falon su kai Alwala sun fito harabar gidan Zulƙi ya shiga ya kira yaranshi maza uku suka wuce masallacin dake manne a jikin gidan ta waje. A cike masallacin yake sosai kundai san jama'armu basai an karashe ba. A cikin masallacin Sai ga ƙafa da kafaɗun Gwadabe manne dana Yaya Hambali. Duk su biyun basu lura da hakan ba har saida gwadabe ya kalli ƙafar ya gane wannan ai kafar Yaya Hambali ce. Da sauri ya ɗago ya kalleshi a lokacin har an yi kabbara. Idanu suka haɗa wani irin kallon tsana Hambali yake jefo ma Gwadabe idanunnan nashi cike dam da farin kwalli kamar yadda ya saba, a yanzu ma yafi rambaɗawa sabida ya samu wadata. hannu yasa ya jawo wani saurayi daga sahun gaba ya sashi a gurbinshi, shi ɗin ya koma sahun gaba. A sanyaye Gwadabe ya ɗaga hannu yace. "Allahu Akbar" Jikinshi sai rawa yake yi dai, haka gabanshi yake ta faɗuwa har aka idar da sallar. Kallon saurayin dake kusa dashi yayi sai yaga Ashe Nazifi ne babban yaron yaya Hambalin. Sauke kai kawai Gwadabe yayi baya ma so ya kallesu zuchiyarshi ta idasa karyewa. Shi dai yana gefe a zaune Zulƙi yanata gaggaisawa da jama'a. Ya jima sosai kafin ya samu kanshi ya ƙaraso inda su Bara'u suke jiranshi. Gwadabe yana ganin yadda Yaya Hambali yake ta girmama Zulƙi. Yayi ƙiba ya sake kyau na musamman, fatarshi ta murje shi da Zulƙi suka saje. A gaban idonshi suka fita shi da Nazifi. "Kuyi haƙuri na barku. Haka muke fama da jama'a, kuma dole kabi dasu inba haka ba sai zagi da cin mutunci. Kuzo muje can gidansu Baba mu gaishesu* Dunguma suka yi gidansu Zulƙi aka gaggaisa akai zumunci. To su dai a gidan suka rabu dashi akan sai Gwadabe ya kawo matanshi sun gaisa. Suna tafe suna tattauna abinda ya faru a masallaci sai gasu a ƙofar gidansu. Babala na daga ta cikin ƙofar gidan, Yaya Halima da Yaya Hambali suna daga ta waje. Gabaki ɗaya sai guiwowinshi suka sake ya tsaya cak shi bai jeba shi bai wuce ba. Kallon kallone ya shiga tsakaninshi da Babala na wasu sakanni. Ganin Babala ta ƙurama waje ɗaya idone yaja hankalinsu Hambali suka juya. Daidai lokacin da Bara'u yake jayeshi. "Ka daure kayi ƙoƙarin cinye jarabawarka Gwadabe" "Daya daure da kar ya daure duk ɗaya. Tsiniwace a kanshi ai inya tako mana gida. Tuni muka tsame matsiyaci a cikin zuriyarmu. Karka sake matanka ko wata banzar tsarabarka ta shigo gidannan. Dan naga Sakina na zagaye da iyalanka" Cewar Yaya Hambali kenan, cikin ihu da ɗaga murya yake maganar tashi. Kuka Gwadabe ya fashe dashi Bara'u ya jashi suka koma gida babu ma kowa a gidan a tsakar gida suka zauna jigum_jiugm sunata jimantawa juna. Har akayi kiran sallar la'asar babu wanda yace da wani uffan har suka fito daga masallaci. A gindin bishiyar mangwaro suka zauna akan kututture. "Gwadabe kayi haƙuri ka ƙara. Uwa ba abun wasa bace, ka kiyayi Babala karka cuci kanka taima baki. Tunda bata son ganinka ni kam in dan ta mune karka sake kawo mana ziyararma wallahi mu mun yafe Gwadabe ka zauna zamu dinga zuwa duk ƙarshen shekara " Gaga_gaga haka wunin ya kasance musu. Sai yamma suka samu shiga gidansu Shafa a tsakar gida suke a zube Abba sai kuka yake yi sabida zafi. Shafa tun rana take sa ran zuwan Gwadabe abincin rana ma data girka ma su Hadiza saida ta ɗebar mishi ta adana da taga har an ɗaura sanwar dare bai shigo bane ta cinye abincin. Gaggaisawa akayo da matan gida, Shafa ta miƙo mishi Abba dake ta raraka kuka "Kukan zafinne haka? Ga ƙuraje duk sun feso mishi, me kike shafa mishi to?" Gwadabe ya tambayi Shafa. "Hodar moju nake barbaɗa mishi, bari in ɗakko a kuma shafa mishi" Ta tashi taje ta ɗakko hodar Gwadabe da kanshi ya shafe jikin yaron da hodar, baifi minti huɗu ba yayi baccinshi a jikin Baban. Matan gidan sai suka tashi suka koma zaure dan cikin ɗaki gaskiya baya shiguwa. Tuwo Shafa ta kawo musu suka taɓa dan sun san su Sakina ma suna can suna jiransu da abinci. "Gwadabe dama ranar da muka zone saina shiga gida wajen Babala. To gaskiya abinda ya faru ya mugun ɗaure mun kai. Yadda Babala taci mutuncinmu, har Abba bata ƙyale ba dan ashe an faɗa mata sunan Baba yaci. Wai bata yafe ba da kasa sunan Baba. "Ya'isa Shafa. Kuma kar in kuma jin bakinki akan wannan maganar. To fa wata sabuwa su Babala manya. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI. NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (8) IYABO Zuchiyata sai naji tana wani irin fusga. Labarin da Baɗɗo take bani ya jijjigani tsoro ya sake shigata sosai, ni dai har muka isa inda zamu hau acaɓa ya fitar damu jere bonyo bance komai ba. A lokacin kawai na riga da nayi saranda na yarda Hama ta ruguzamun rayuwata. Muna isowa jere muka soma cin karo da matan ƙauyanmu masu nono. Nan ƴan gulmammakinmu na mata ya soma tashi, har a bayan akori kura wata ƙawar Hama saida ta kasa haƙuri ta tambayi Baɗɗo. "Baɗɗo hatsari yayarki tayi ne naga fuskarta a kumbure idonta ya tara jini baƙi ga bakinta a fashe?" Ɗagowa nayi na dubeta, na dawo da kallon nawa zuwa ga Baɗɗo. "Zamewa tayi a bayan gida shine taji mummunan rauni asibiti ma zamu je" "Asibiti a cikin ƙauyannan ana zuwa asibiti dama?" Ni dai takaina nake yi, dan ni a lokacin wallahi ji nake kamar kaina zai faɗo, ga wasu jijiyoyi da suka ɗaɗɗaure a kaina sai nake jina wani iri haka. banma dawo hayyacina ba har saida naji motarmu ta kawo kan iyaka mun iso Girei. Da ƙyar na sakko jiki duk ciwo, ko ina yayi tsami ga ciwon baya ya far mun. Mun jima a titi kafin muka samu bus ɗin da zata shiga gari. Wayata na zaro a jakata na kunna a lokacin rawar ɗari ma nake yi. Muna shigowa Adamawa kafin ma mu sauka na danna kiran wayar Uwani. Nako taki sa'a ringi biyu ta ɗauka. "Kaga Amarya ƴar gaban goshi, shalelen Hamma, yau an fito birni kenan?" Idanuna na lumshe hawaye suka zubo mun da ƙyar na ɗan saisaita nutsuwata nace. Uwani ki roƙi Hafizu dan Allah ya barki kizo. Wallahi ina cikin matsala, abubbuwa da yawa sun faru yanzu haka mun shigo garine Baɗɗo zata kaini asibiti, zaiyi wuya su sakeni in koma gida ma yau." Sai na fashe mata da kuka duk na tashi hankalin Uwani. "Shikenan Iyabo. Yanzu zan shiryo in tawo, zamu dinga waya har in iso. Kiyi haƙuri koma menene zanzo zamu samu mafita in sha Allah " Wayar na datse ina share hawayena wasu na zubowa. Ni hama zata sama wari a jiki, ta rabani da Hammana, to dama shi kishin haka yake, ko kuma a ƙauyen haka suke nasu kishin na azaba? Ya Allah ka ɗauke mun wannan lalurar warin da aka ɗauramun Allah ka bi mun kadina" Idanu na runtse zafin idon daya tara jini har tsaƙiyar kwanyata babu shiri na buɗe. Motarmu ta sauke mu a bakin tasha, acaɓa muka tare zuwa bakin asibiti. Muna bakin asibitin Uwani ta kirani motarsu ta baro kano. Mu kuma muka shiga ciki, Baɗɗo ta zauna mun a layi ni kuma na buɗe fayil na yanki kati. Akwai layi bana wasaba haka mukaita bi. Saida wata mace tazo wucewa ta ganmu a layi ta dubi idona tace. "Likitan idanu kuke son gani, dan naga idanunki suna ciwo sai ruwa kuma suke zubarwa?" Nace da'ita. E likitan ido nazo gani" "To ku biyoni, nan ba ɓangaren masu lalurar idanu bane. Kuzo muje" Haka duk uban layinnan da muka bi ya tashi a tutar babu. A baya mukaita binta har ɓangaren masu lalurar idanun. To mun kuma yi latti, da ƙyar wannan matar dai ta samu a layi dan taga idanun ya matsa mun. Mune har bayan azahar bamu shiga ɗakin ganin likita ba, sai wajajen uku saura aka kirayi sunana. Baddo na barma jakata da wayata na shiga ofishin likitan idon. Izinin zama ya bani, ya ɗago ya dubi idon da kyau kana yace. "Me ya sameki, dukanki akayine, ko me ga idon yanata zubar da ruwa?" Faɗuwa nayi a banɗaki shine na faɗi idona da bakina suka daki gini" Girgiza kai yayi yace. "Ashsha, Allah ya kiyaye gaba. Ga gado zo ki kwanta inason duba lafiyar idanun" Bayan na hau gadon sai yaga jikina na wani irin ɓari, ni kaina ɓarin da jikin nawa yake yi saiya tsoratani. Ba shiri ya taɓa jikina yayi wani irin mugun zafi, ni dai nasan inajin gadon dana kwanta yana juyi dani. Daga haka ban sake sanin abinda ke faruwa ba. Ban sake samun kaina ba sai farkawa nayi naga ledar ƙarin ruwa a hannuna. Baɗɗo na zaune a ƙasa, Uwani na zaune a kan gadon da nake sun ƙura mun idanu. "Ta farka Baɗɗo. maza jeki ki kirawo likita. Iyabo sannu yaya jikin?' Uwani har kin iso ashe?" Da faɗar haka saita soma share hawaye, murmushi nayi nace. Ki dena kuka, tawa jarabawar ta wannan auren kishiyace Uwani. Wai yau nice a gadon asibiti, namijin da nafi sonshi fiye da kowa shi ya dokeni, banda wari da matarshi ta saka mun. Jarabawar da girma Uwani. Amman akwai Allah " Shiru Uwani tayi ta kasa cemun uffan. Niko wani tawakkaline naji ya shigeni ainun, lammurana suna ga Allah. "Tun jiya muke asibitinnan Hamma baizo ba, matar tashi ma bata zo ba ko leƙe. Surukarki dai ta zo jiya sai wajajen magriba ma tabar asibitin. Dada kuma basu san halin da kike ciki ba,haka Baffa Musa, saidai Amaduyal ya sani. Kinga shi ya kawo mana abinci jiya, da safennanma shi ya kawo mana. Iyabo na tausaya miki. Amman wallahi kinsan Allah saina rama dukan da Hamma yayi miki a jikin figaggiyar matsiyaciyar matarshi?. Ƴar iska ke da zaki zage ki ci ubanshi ko da asiri da kin matseshi gobe bazai tunkaroki da duka ba. Jibi yadda ya nakasaki fa Iyabo . Taya zan tsaya wani ɗan ƙauye jahili yaimun irin wannan dukan, wallahi ko ya fi karfina da cizo, da yakushi saina kwaci kaina, in haɗa da hauka." Idanu na lumshe kafin in buɗe likita ya iso shi da Baɗɗo. "Sannu Jabu. Yaya yanayin jikin naki kike jinshi?" Ko ina ciwo yake yi mun. Kaina kuma yana matsanancin ciwo, ga wata jijiya da tai tsaye ta saman idon ciwo take yi mini" "Ki nane idonki mai lafiyar marar lafiyar ki barshi a buɗe" Umarninshi nabi, amman me koda na toshe idona mai lafiyar na bar marar lafiyar a buɗe dishi_dishi kawai nake gani" "Kina iya tantance kalar kayan jikina?" A'a gaskiya baƙi nake gani babu kala" Sai naji kuka na shirin kamani. "To to Shikenan sake hannunki, ki biyoni zamu je ɗakin gwaji, domin musan a wanne mataki ciwon yake. Karin ruwan dake hannuna ya cire mun" Uwanice ta taimakamun na sakko akan gado. "Baddo ki zauna ki jiramu, zan rakata" Cewar Uwani kenan. Tare da'ita muka shiga cikin ɗakin gwajin. Abubuwa mataki_mataki akaita bi. Har Abcd aka nuna mun a allo akace in karanta, in ban iya karatunba in ina ganinsu da kyau in sanar. Aka sakamun tabarau a idona, asa wannan a cire wannan, harda tocila saida aka haskamun idona likita sai tambayoyi kawai yake yi mun ina bashi amsa. "To Shikenan zaku iya komawa. Ƙila zamu sallameta zuwa anjima ko kuma gobe da safe" Jijjunanmu a mace murus muka dawo ɗakin jinyar. Muka tarar da Yafendo ta zo." "Jabu sannu da jiki" Yauwa Yafendo sannu da zuwa, ai da kin yi zamanki" Na zauna akan gadon kaina a ƙasa. "Ban isa in zauna ba, wallahi jiya ko baccin kirki ya kasa zuwarmun." Uwani tace. "Haura ki kwanta Iyabo sabida yanayin jiki" Sai data taimaka mun na kwanta, suka gaisa da Yafendo, ta tambayesu yanayin jikin. "To kusan dai zamu ce ido kam ya samu matsala, dan inuwa take gani dashi. Yanzu haka daga ɗakin gwaji muke. Sai dai muce Allah ya bata lafiya ya bata haƙuri dan matsalar idanu tana daga cikin manyan matsaloli kusan zamu iya kiranta mutuwar tsaye. Sannan fa Yafendo har yau Hamma ko matarshi babu wanda ya leƙo asibitinnan. Ni cewa nayi sun san Iyabo bata da lafiya kuwa?" Salati Yafendo ta saki tana tafa hannaye. "Uwani kina nufin Hamma baizo ya duba jikin Jabu ba?" Uwani tayi ƴar dariya tace. "Baizo ba wallahi, kinga dai tun jiya nake asibitinnan" Shiru Yafendo tayi ta kasa cewa komai harna tsawon muntuna masu dama. Har wata ma'aikaciyar jinya tazo ta mayar mun da ƙarin ruwa, aka diga mun magani a idona. Har zuwa lokacin Yafendo bata ce komai ba." "Jabu, cuta ce an riga an cutar dake tunda kome za'ayi a matsayin ɗaukar fansa ba zai goge wannan lulurar data sameki ba. Amman ki sani wannan yaron bashi da laifi yi mishi akayi. Ita kuma Hama zan ɗauki mummunan mataki a kanta matakin da hatta iyayenta bazai musu daɗi ba. Dan Allah kiyi haƙuri kuma a rufe wannan sirrin bana so Daso, da Baffa Musa, da su A'i suji. Mu haƙa daku mu burne. Shi kanshi Hamman a hakan zaiga fishina da ɓacin raina. Ina zuwa zanje wajen aikinsu in sameshi" Nayi juyin duniya Yafendo ta bari karta je wajen aikin su Yaya Hamma, ko saurarena batai ba ta fice a cikin fishi tea Uwani ta haɗamun. "Tashi ki sa wani abun a cikinki. Ai gara ki bari taje ɗin. Duk da ana zargin farraƙu akayi musu, baya nufin za'a zuba ido. Narantse da Allah idona idon Hama saina sabautata na nakasa wani shashe na jikinta in da daɗi sai taji" Baɗɗo tace. "Koni ɗazu dana koma gida da safe saida mukai rikici sosai da'ita. Yuguda ne ya jayeni zuwa ɗaki naso in daketa ne, amman ban samu dama ba. Na barota a gidan ita da Daso tsohuwar munafuka, ita take kaita wajen bokaye tun kina Makka lokacin" Ni dai ina zaune ina shan shayi, duk wacce tayi magana in kalleta. Sun ɗauka da zafi. Ni inata gwada musu abi komai a hankali abinda haƙuri bai bayar ba, tashin hankali bai isa ya bayar ba. Ina gama shan tean Uwani ta zubo mun jallof ɗin shinkafa mai bushasshen kifi. Loma biyu kawai na iya turawa na danne da ruwa. Ruwan hannuna na ƙarewa aka ciremun saina fita nayi alwala ina daga zaune a dadduma na soma rama sallolin da ake bina. Ban idar da sallar ba saiga Yaya Hamma Yafendo ta tasoshi gaba sunzo. Suka gaisa da Uwani ba yadda suka sababa, dan a daƙile yake magana, kuma ya cusa hancinshi a cikin rawanin daya naɗe kanshi dashi. Uwani kuwa sai harara take zabga mishi tana mai kallon wulaƙanci. Ina sallamewa na ɗago na dubeshi, sai naga ya sake mun kyau. Shima idonshi yana kaina bai ɗauke ba. "Sannu yaya jikin naki, ashe baki da lafiya?" Nan Yafendo ta shiga yi mishi faɗa da yare, sai ruwan faɗa take yi inaji tana ambaton Hama dai. Shuru yayi baice mata komai ba. Uwani da Baɗɗo sai haƙuri suke bayarwa, ni dashi munyi shiru muna kallon juna, ina hango tausayina a cikin ƙwayar idanunshi. A cikin kallon ƙudan da muke yima juna a zuchiyata ina roƙon Allah ya karya mugun asirin da Hama tayi mana domin mu samu zaman lafiya" Ana cikin haka likita ya shigo da takaddar sallama ya miƙama Hamma. Jiki a mace ya fita. Likitan ya dawo da dubanshi gareni. "Jabu mun sallameki. Amman duk bayan kwana talatin zaki ci gaba da zuwa muna duba lafiyar idanun naki. Zamu ɗauraki akan maganin ɗigawa safe, rana, dare. Sannan ki guji gasken rana, kuma karki dinga jagwalgwala idanun. In sha Allah karku saka damuwa a zuchiyoyinku idon zai warke, ba mutuwa yayi ba, matsalace kawai amman indai muka ɗaurata bisa magani zai farfaɗo da jijiyoyin idanun da suka sandare. Wannan taruwar jinin ita kuma ba wata matsala bane da sannu zai washe" Haka dai wannan likita yaita ƙarfafani da bani shawarwari. Yaya Hamma yana dawowa daga biyan kuɗin sallama, ya miƙo ma Baɗɗo ledar magunguna, suka harhaɗa kaya muka fito. A mota ya ɗauramu ya biya kuɗin. Mu muka kama hanya, shi kuma ya koma bakin aikinshi. Ga ciwo ga rashin kyan hanya. Bamu muka isa jaɓɓi ba sai yamma sakaliya. A tsakar gidan duk muka samu matan gidan dawowarsu daga talla kenan. Hama na wanke_wanken kwanukan tuwon jiya tana ganinmu ta wani taɓe baki. Uwani na riƙe dani wallahi ban ankaraba naga kan Hama a cikin bokitin ruwan wanke_wanke Uwani ta dulmiya mata. Da ƙyar Hama ta samu ta kwaci kanta dambe ya kaure na tashin hankali tsakanin Uwani da Hama. Matan gidan sun kasa raba wannan faɗa dan Uwani ta mahaukaci tayi musu, duk wanda yazo kusanta saita gabɗa mishi kwano. Saida fa maƙota suka cika gidan wannan faɗa ya rabu da ƙyar. Duk Uwani ta fashe ma Hama Baki, har nono uwani ta riƙe ma Hama kamar zata tsige mata shi, Hama sai ihu take faman yi. Ita kuma Hama ta gama yakushe ma uwani fuska sai jini suke zubarwa. "Wallahi tun wuri kije ki tone asirin da kika ma Jabu. Shegiya muguwa mai baƙar zuchiya kawai, bagidajiya. Ku kuma munafukai ƴan iska ƙyaleku Jabu tayi wallahi dani nake aure a gidannan duk saina saisaita muku zama." Hama dai babu bakin Magana sai haki take ta famanyi. Dan iyakar dakuwa wallahi ta daku ainun. Da ƙyar matan unguwa suka tunkuɗa Uwani ɗakina. Yafendo ta dubeni tace. "Jeki Jabu ki kwanta ki huta. Ke kuma Hama ki tattara ki koma gidanku. Kuma kiyi gaggawar karya asirin da kika yi mata. Ki sani Jabu ɗiyatace ko a gidan wani take aure sai inda ƙarfina ya ƙare wajen ƙwatar mata hakkinta. Balle kuma ɗana take aure. Kece bare a cikinmu dan haka kiyi gaggawar ficewa a gidannan" Ni dai naji daɗin dukan da Hama tasha, kuma raina yayi fari da hukuncin da Yafendo ta yanke. Ɗaki na shiga na samu Uwani sai fito da kayan ɗakina take yi. "Iyabo ga kujera a tsakar gida ki zauna akai ko ki kwanta. Saina caje ɗakinnan tsab na zaƙulo abinda aka ajjiye a ɗakin." Zama nayi a kujerar ina kallonsu ita da Baɗɗo sai zaƙule zaƙule suke yi, amman fa an fitar da gabaki ɗaya kayan ɗakin babu komai. Uwani ta miƙo mun fulo, kafin in amsa sai naga ta cire fulon a riga. Hmm mutum abun tsoro saiga fulo a ɗan farke. Uwani da ƙarfi ta kama fulon ta yage saiga jar laya a ciki. Ba shiri na miƙe na shiga ɗakin bakina a buɗe" "Kingani ba Iyabo. Lallai wannan kishiyar taki tsinanniyace. Ya tabbata ita tayi asirin rabaki da Hamma harya dikeki haka. To Alhamdulillah asirinta ya tonu, kuma na rama miki dukan da tai miki itama yanzu zanje in kuma cin ubanta" Zabura uwani tayi, nayi saurin tarota da ƙyar uwani ta yarda ta haƙura ta bar Hama haka. Uwani yanzu yaya zamu yi da wannan layar to?" "Buɗewa zamu yi, mu ƙona komu jefata a masai" Baɗɗo tace. "A jefa a masai kawai basai an buɗeba, ni tsoro nake ji. Amman a nuna ma Yafendo tukunna" Nayi carab nace. A'a kar a nuna mata. Hankalinta zai tashi da yawa. Kuma ƙila hakan yasa ta tursasa Hamma ya sau matarshi" Wata uwar harara Uwani ta bini dashi tace. "Au ke kinfi so ku zauna tare, an ganota ta nan taje ta kuma ƙullo sabon asirin da bakisan ma ko rayuwar zata rabaki da'ita ba. Wai bake kika ce mun kinsha kama garukan magani a ruwan wankanku, ko banɗaki ba, bake kika faɗamun ko abincinta ran girkinta taki miyar sai an barbaɗo miki magani ba. Iyabo anya kinsan ciwon kanki kuwa?" Uwani tabalbalin kenan ƙawar faɗa da daɗi. Murmusawa nayi ina hawaye. Uwani bawa mai cikakken imana yadda yake da ƙaddara imma mummuna, imma kyakkyawa. Na daga cikin sunnar rayuwa, rayuwa bata taɓa tafiya face sunyi kafaɗa da kafaɗa da matsaloli tari daban_daban. Ni bazan so in kashe auren Hama ba in ɗauketa daga kan yaranta ba. Duk mummunan halina bazan so Hama ta fitar dani a gidana ba. Wallahi in halinta ne dama ki rubuta ki ajiye zata kuma. Watarana shi shaƙundun ɗinne zai kamata da idonshi. Anan yana da damar zama da'ita ko rabuwa da'ita." "Ahh haba dan Allah? Ai kamata yayi a mayar da layar cikin fulon kawai. Kinga watarana Hamman da kanshi zai gano layar" Dariyar dole tasani, itama duk da a cikin ɓacin rai take saida ta dara. Miƙo mun layar tayi da bismillah a bakina na karɓa na jefa a masan gidan. Alwala nayi a bakin rijiya na wuce bukkar Yafendo na yi sallar magriba da Isha. Nasha magunguna, na ɗiga na idon. Yafendo ta dure mun tuwo tace. "Maza ki daure kici tuwon Jabu. Sai kiyi kwanciyarki, in bacci ma ya ɗaukeki sai ki kwana abunki. Ina tsaka da cin tuwon Yaya Hamma, da Haruna mijin Safiya suka shigo. Gabaki ɗaya hankalin Yaya Hamma a kaina yake gaba ɗaya. Zama yayi yana fuskantata, ɗagowa nayi muka haɗa idanu. Kallon da yake yi mini mai cike da fassarorine masu dama, saƙone daga zuchiya zuwa ga zuchiyar da ake so da ƙauna. "Yaya jikin naki, ki cire hannu a tuwon bari in siyo miki nama ki ci" A jejjere yayi maganar cike da kulawa tsantsa. Idanu na lumshe a raina nace. Tsarki ya tabbata ga Ubangijin daya kuɓutar da Annabi Yusuf daga cikin rijiya. Kuma yasa wuta ta zama ni'ima ga Babanmu Annabi Ibrahim." "Dada bari inje yanzu zan dawo zan kawo ma Jabu nama ne" Ya fice da sauri ba tare da yaji me Yafendo zata ce ba. Murmushin farin ciki naga tana yi. Niko farin cikin da nake ciki bazaima musaltuba sam, sai ajjiyar zuchiya nake saukewa. Yaran Hama ne suka shigo. Mai sunan Yafendo riƙe data goyen, ta tsakiyan na biye dasu ashe Hama bata tafi da'ita ba. Karɓarta Yafendo tayi ta goya su kuma ta zuba musu tuwo suka zauna suna ci. "Assalamu alaikum. Yafendo sannunku." Cewar Uwani kenan tana daga bakin ƙofa. "Yauwa am Uwani. Kun gama kwalimar ne?" "E mun gama shine nazo kiran Jabu ta kwanta" "Gaskiya ne. Jabu kije ki kwanta, kar ki tayarma da mijinki wata maganar ɓacin rai. Kibi dashi kamar babu abinda ya faru. Sauran ki barmun a hannuna. Tashi kije Allah ya ƙara karewa" Kaina a ƙasa nace. To Shikenan Yafendo saida safe, Haruna saida safe" Haruna dake zaune tunda ya shigo baice komai ba yace. "Allah ya ƙara sauƙi, ki yi haquri da abinda ya faru. Bamu da shaidar dukan mace a gidannan. Akwai dai wata maƙarƙashiya a ƙasa, kinsan sha'aninku na mata sai haƙuri. Na dawo tun daga hanya aka tareni ake faɗamun wai anyi dambe gagarumi a gidannan wai dake da Hama. Yaya Hamma ma an bashi labari har tafiyar Hama gida duk yaji." Murmushi nayi nace. Nagode Haruna. Sai da safe" Nai musu sallama nabi bayan Uwani har zuwa ɗakina. Sun kuma sake ma kan gadon nawa wajen zama. Kwanciyata ke da wuya muka jiyo sallamar Yaya Hamma ya shigo tare da abokinshi Baɗejo. Waje Uwani ta basu suka zauna. "Ga wannan naman Uwani kuci ke da Jabu." Uwani tasa hannu ta karɓi ledar. Mayafi na sako na fito daga cikin labulen da gadona ke ciki muka gaisa da Baɗejo. Shiru ya ɗan biyo baya can dai Baɗejo yace. "Jabu, ni bansanma ta ina zamu soma baki haƙuri ba. Amman duk da haka kiyi haƙuri abinda ya faru dan Allah ki ɗaukeshi kamar ba'aiba. Ni wallahi da badan Hamma da bakinshi ya labartamun abinda ya faru ba. Alƙur'an da duk wanda ya faɗa mun wannan maganar bazan yarda ba. Shi kanshi yace baisan sanda abun ya faru ba. Kiyi haƙuri ki mishi afuwa dan Allah. Ki dubi girman ƴan uwantaka da soyayyar da Hamma yake yi miki kiyi haƙuri. Sannan naji labarin iftila'in daya afka ma daddobinki. Allah yasa da abinda ya tare. Munji labarin faɗan daya ɓalle a tsakanin Hama da ƙawarki Uwani. Uwani ayi haƙuri dai dan Allah koma me ake tunani bazai wuce zargiba. Ita kuma Hama koma me zata yi a wannan gaɓar bazai wuce kishi ko zigazigin ƙawaye ba." Baɗejo ya daɗe yana tausata. Mai gayya mai aikin yayi tsamo_tsamo duk kunyata ta lulluɓeshi. Ni dai nayi ɗan guntun murmushi nace. Babu komai Baɗejo wallahi na yafe. Kuma wannan abun daya faru bai rage son da nake yima Hamma ba saima ƙaruwa da yayi. Tunda har yasan yayi laifi ya kuma ɗakkoka dan kawai a bani haƙuri na haƙura. Batun dabbobi kuma Allah yasa da abinda suka tare" Naja bakina na tsuke. Ajjiyar zuchiya Yaya Hamma ya sauke a sirrance. Shima haƙurin ya kuma jaddamun dai, nace komai ya wuce. "To komai ya wuce Hamma. Ina mai baka hakuri a bisa dukan da naima matarka. Dokin zuchiyane yasa har abinda zai faru ya faru. Saimu haɗu mu yafi juna" Cewar Uwani kenan. Yaya Hamma yace. "Ai babu komai daliline nasan dole yasa faruwan hakan." Nan Baɗejo yayi mana sallama, Yaya Hamma ya tafi rakashi yace mun daga nan zai je yaba Yafendo haƙuri akan laifin da ya aikata. Kuma ya bata haƙuri Hama ta dawo ɗakinta. Ruwan tea Uwani ta dafo mana muka baje tsirannan. "Iyabo naga akwatin aurenki a mugun yashe. Nace kyautar da kayan kika yi, kome kikayi ke ko da su?" Nadai san kala huɗu kika bani in dinko miki, kuma na tawo dasu ma an daɗe da ɗinkawa. Mamaki dam fuskata na dubeta. Bance komai ba na miƙe naje na buɗe akwatunan kusan rabin kayan babu. Da hanzari na buɗe sib na ɗakko akwatin ƙarfen da kuɗina suke ciki. Dama tunda na ɗakko naga kwaɗon a ɓalle gabana ya faɗi. Babu ko ficika a ciki. Salati kawai na shiga jejjerowa ina jijjiga kai Hama naga halama so take ta sabauta mun rayuwata. Uwani ce ta iso inda nake da sauri. Uwani harda kuɗaɗena masu yawa duk kinga an kwashe mun. Wallahi nasan kuma Hama ce zata yi mun wannan aikin. Har kayan akwatinma itace zata kwashe. Illar rashin ƙofa kenan. Dole Yaya Hamma yaimun ƙofa gaskiya. Yanzu Shikenan fa ta kassarani gabaki ɗaya jarina ya ruguje murus" munfi minti talatin a Zazzaune muna jimami. A cikin wannan halin Yaya Hamma yazo ya samemu, cikin tashin hankali yake tambayar meke faruwa. Uwani ta miƙe ta nufi hanyar waje. "Matarka zata maka bayanin abinda ke faruwa. Ni kam saida safenku." Tana fita ya dawo kusa dani, ganin duk ya ruɗe na fashe mishi da kukan baƙin ciki wanda ya sake sukurkutashi. Sai kuma ya mugun bani tausayi har sauya launi idonshi yayi. "Jabu kiyi haƙuri in akan abinda nayi miki ne. In akwai wani abun ki sanar dani dan Allah" Nan cikin kuka na faɗa mishi satar da akaimun. Kai tsaye ban halaƙanta satar da matarshi ba. Kai ya girgiza yace. "In dan akan wannan ne kike wannan kukan gashi ke ba cikakkiyar lafiya ba. Kiyi shiru ni zan biyaki kuɗin da aka sace miki, da kuɗin kayan da aka sace mikin Shikenan in anyi hakan kukan zai ƙare? Ko nawa aka sace miki kuɗinki bazai yi ciwon kai ba zan biyaki" Faɗawa nayi ƙirjinshi ina share hawayena tare da kuma shigewa jikinshi. Danna lura saifa nayi da gaske zan iya zaman aure a ƙauyannan. Jibi yarinya ƴar ƙauye duk ta hautsina mun lissafi, ta kwance mun notukan kayina. A wannan daren ni naga soyayya da tattali ra'ayul aini. To anan nake cewa sai Allah ya kaimu ranar Talata kuma dan ranar monday akwai hutun maulidi oga na gida ba zaku samu posting ba sai ya koma aiki talata. MRS BUKHARI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (9) Takai: Ba shiri Shafa ta bar zancan ganin yadda Gwadabe ya ɓata rai. "Munga tsaraba an gode Allah ya ƙara buɗi. Duk an rarraba ma kowa. Sannan kaima Yaya Bara'u godiya tunda muka shigo Takai kullum sai an aiko su Toye da ƙunshin tsire ko balango" Bai amsaba ya miƙe tsaye. "Bara'u muje ko? Zamu tafi sai da safe. Gobe zanyi wata ƴar tafiya amman a goben zamu dawo, ina buƙatar adda'a " Ya ciro kuɗi a ajjihunshi ya bata. "Ga wannan nasan ba zaki rasa abun saye ba. Gobe kije gidan Sakina ki wuni tare da Hadiza, itace baƙuwa a garin" Nan sukai mata sallama, kai tsaye masallaci suka nufa suka sallaci magriba. Sai gasu a majalisar abokai nan akaita hira zuwa isha, da sukai isha suka shiga gida da ƙumshin nama, Bara'u ya aiki yaro ya kaima Shafa nata kason. Gwadabe fa tun haɗuwar da yayi dasu Babala har yanzu ita ke yawo a kanshi. Sukuku haka ya shiga gidan ya tarar da su Sakina da Hadiza da yaran duk anata cin abinci. Shinkafa da miya harda latas suke ci. "Gwadabe wannan nisan kiwo haka. Tun fitar sassafe ko abincin ranar ma baku shigo kunci ba. Kai ku ba iyayenku waje, ku dawo tanan" Yaran suka dawo inda Sakina ta nuna musu, iyayen kuma suka zauna a wajen. Hadiza dai taga mijinta duk ya canja abunka da mace mai shegen kishi sai zuchiyarta take raya mata dan yaga Shafa da Abbane, shine ita da ummi ya sharesu. Tunda tace mai sannu da zuwa bata kuma tankawaba. Gwadabe kuwa da ƙyar yaci abinci loma biyar, a hakanma Bara'u ke ta janshi da hira. "Gwadabe nace naga kayan da Anty Badi'a ta aiko mun dashi. Nagode sosai Allah ya bar zumunci. Hadiza ma ta gwangwajeni da kayan mutan nijar, Allah dai ya bar wannan zumunci har gidan aljanna" "Ameen Sakina babu komai. Wata rana haka zamu zama surukan juna kinga an sake curewa an zama abu ɗaya" Ɗan darawa akayi Hadiza tana zaune kamar dutse ummi harta soma kuka taƙi kulata ga yarinyar a cinyarta, sai cin abincinta take. Gwadabe da dama a hasale yake wajen saukewa yake nema yace. "Kinaji yarinya duk ta cika mana kunnuwa da kuka ki bata Mama mana ta tsotsa" Da fishi Hadiza tace "Nima fa abincin nake ci kana gani. Yarinyarnan yanzu tasha ni babu wani nono da zan bata" Dama Hadiza tayi ne akan ramuwa, batasan kura ta kwanto ma kanta ba. Duk da bai kulata ba face miƙewa da yayi idandunanshi suka kaɗe. "Sakina zanje in kwanta kaina ciwo yake yi. Gashi gobe zamu shiga Kano" A razane Hadiza ta kalleshi ya daka mata harara yayi ficewarshi ya ɗaura mata tention shi kanshi yaga hakan. Sanyin bishiyoyi masu kaɗawa da ƙamshin korayen ganyayyaki ne yasa Gwadabe wani lafiyayyen bacci, duk da ranshi da zuchiyarshi a jagule suke. Washe gari sassafe su ka yi wanka. Suka karya da alala da kunu mai zafi Gwadabe ya mike yace. "To Hadiza, Sakina mu kam zamu ɗau hanyar Kano sai in Allah yayi dawowarmu. Shafa zata zo ta wuni tare daku anan. Dan Allah Sakina ki shiga dasu gidan Zulƙi. Ko kuma su jira inna dawo sai in gaisu in gabatar dasu" Har sun fito ƙofar gida ya jiyo muryar Hadiza. "Gwadabe dan Allah bani minti biyu" Murmushi yayi yasan za'a rina. Yana zuwa ta sauke murya tayi kalar tausayi. "Jikina yana bani gidan tsohuwar matarka zaka je. Wai dan Allah sai yaushe Iyabo zata barmu mu mori mijinmu ne? Jiya na kasa runtsawa sabida tunani, duk da ba yau Iyabo ta taɓa sani nai asarar darena ba. Amman abun ya haɗemun harda canjin dana gani jiya a wajenka sabida kana zumuɗin ganin Shafa da Abba" Kallonta yake tayi tun sanda ta soma Magana. Da dariya ya fashe da yaga kuka take ƙoƙarin yi. "Hadiza Matata ta kaina. Iyayen kishi su da kansu. Yafa kamata ki dena yadda da duk abinda zuchiyarki zata rayo miki gudun faɗawa tarkon dana sani. Iyabo ta tsone miki idanu da yawa naga ko Shafa dake ainihin kishiyarki abokiyar gurzawa bakya kishinta rabin yadda kike kishin Iyabo, ya kamata ki kama muguncinki, karki bari ki sire mun. Mu zamu tafi karmu makara" A tsaye a ƙwar gidan ya barta bata shige ciki ba har saida suka ƙule ta ja jiki a sanyaye ta shige hantar cikinta sai kadawa take yi" Kano:. Saukarsu Gwadabe ke da wuya a garin Kano suka wuce unguwarsu Iyabo gidansu Uwani. Mahaifiyar Uwani Hajiya ce ta fito. "Au Gwadabe shine kuka tsaya a waje sai kace baƙi bismillah ku shigo" Dole haka suka kutsa cikin gidan. Hajiya ta shinfiɗa musu tabarma suka zauna aka gaisa a nitse. "Dama Hajiya gidan Uwani muke son yaro ya rakamu." Hajiya tace. "Allah sarki ai kuwa kunyi saɓani Uwani ta tafi Jaɓiɓi wajen Aminiyar tata Iyabo acan take aure, to tafiyar ta gaggawace ma dai. Kuma tunda ta tafi ba mu yi waya ba, yaranta ma suna nan tare dani" Tashi ɗaya Gwadabe ya koma kalar tausayi. Ba baƙin ciki yake da auren Iyabo ba. Ba kuma baiji daɗin jin tana gidan aure bane. Kishine na zahiri wanda bashi da masarrafarshi. Sai yaji ƙirjinshi yayi mishi nauyi. "To Hajiya ko zan iya samun lambar wayar Uwanin ko ita Iyabo ɗin?" "To gaskiya ni babu waya a hannuna. Yara da zasu baku lambar gashi duk kowa ya fice. Sai dai in gobe zaku dawo sai in sa yara su rubuta lambobin a takadda" Bara'u yayi carab yace. "A'a ki barshi Hajiya. Nanda sati ɗaya ma dawo kafin lokacin Uwanin ta dawo sai muzo a kaimu" Hajiya tayi jim tace. "Amman Allah dai yasa lafiya ba wani abun bane ba ko? Naga kamar kun matsa lallai sai kunga Uwanin" murmushi Gwadabe yayi yace. "Babu komai wallahi Hajiya. Dama dai labarin Iyabo muke son ji a bakin Uwani. Baya ga wannan babu komai" Dariya Hajiya tayi irin ta manya tace. "Allah sarki. Ai indan wannan ne ba dole sai kun nemi Uwani ba. Iyabo dai tayi aure a dangin mahaifiyarta. Dan kamar Uwani tace mun da gyatumar yaron da ita Iyabo ta aura. Da gyatumar Iyabo ya da ƙanwa suke. Sun jima suna son junansu tun su Uwanin da IYABO suna Saudiyya. Auren bai jima ba da akayi shi." Sai kallon kallo tsakanin Bara'u da Gwadabe. Gashi babu damar su matsama Hajiya da tambayoyi. Saidai abubuwa da yawa sun cunkushe kan gwadawa. Na farko shine Saudiyya da yaji Hajiya tace tun suna can. Na biyu jin a irin dajin da Iyabo taje tayi aure. Yasan labarin ƙauyen a bakinta amma bai san komai baya ga labarin bakinta ba." "To Shikenan Hajiya mun gode. Mu zamu koma, a isar mana da saƙon gaisuwarmu wajen Uwani dama Iyabon." Cewar Bara'u kenan. Shi kam Gwadabe yana cikin dabaibayi. "Zasu ji. Ya yaran duk suna cikin ƙoshin lafiya dai ko?" Bara'u yace. "Suna lafiya. Suna karatunsu arabi da boko. Hajiya mu zamu wuce to" Bara'u ya zaro jaka biyar ya ajjiye ma Hajiya. Sukai mata sallama suka fito. Suna zaune a motar Takai Bara'u yace. "Wannan shirun yayi yawa Gwadabe me kake nufi ne. So kake IYABO ta zauna babu aure ko me? Naga kai mata biyu ka aura rana ɗaya" A fusace yace. "Na auresu ne a bisa tayin aurensu da akayi mun. Waɗanda sukaimun tayin sun fi ƙarfin komai a wajena. Iyabo itace rayuwata Bara'u " "To itama saika ɗauka umarnin mahaifiyarta tabi tunda ai kaji ance ɗan uwanta ne ta aura. Ni na ɗauka ma Debisi ne zai aureta wallahi" "Hakane Bara'u. Ina tayata farin ciki da auren data yi. Sai dai ina tayata jimamin zaman ƙauye. Dan a yadda take bani labarin ƙauyan ƙauyene ƙayau, gasu da ƙauyanci da ƙarancin addini. Ko asibiti babu fa, balle wutar lantarki, kaga babu ruwa babu kwalta, babu makarantu." Jim Bara'u yayi yace. "Sanin da ba. Kasani ko sun samu tallafin gwamnati. Ita kanta sau ɗaya fa kace ta taɓa zuwa tun tana yarinya. Inka lissafa daga lokacin da taje zuwa yanzu ƙila sun samu ci gaba. Ko shekara biyar baya ka kalli takai ai kasan an samu gagarumin ci gaba ko? Ni batun zuwansu Saudiyya ita da Uwani shi nayi tunanin zaka yi nazari akai ma" Kai Gwadabe ya dafe tare da lumshe idanunshi. Baice komai ba, tunani da lissafe lissafe yake ta faman yi har Allah ya dawo dasu Takai lafiya. Cikin gidan ma daya shiga wani tarin tulin takaici ya tarar. Hadiza sai kumbura take yi kamar kwaɓin gurasa. Sakina da Shafa su kuma sunata faman hirarsu da nishaɗi. Gefe guda Gwadabe ya zauna jigum. "Bara'u Gwadabe ba lafiya ne?" Bara'u ya amsa ma Hadiza da cewar. "Kanshi ke ciwo ga hanya mun shawo" Shafa sai tabar abinda take yi ta koma wajen mijinta ta kai musu abincinsu. Lamarin daya sake zugunɗuma fishin Hadiza ta sakei hawayen da take riƙewa kenan. Ta kullace wannan wulaƙancin da Gwadabe yake yi mata dan yaga ya kawota garinsu. Da yamma liƙis suka dunguma gidan Zulƙi sun ko yi saɓani Zulƙi da iyalanshi basa nan sun tafi wani taro na masu kujeru a hannu a Abuja. Gwadabe ya kwashi su Hadiza harda Bara'u da Sakina suka je. Kwanansu biyu a gidan Tamu. Ayashe itama ta tarbesu tarba me kyau sosai. Nan da aka haɗu dole saida labarin Iyabo ya ratso ta cikin zancan. Hadiza tana mamakin irin tasirin Iyabo a cikin rayuwar Gwadabe da duk makusantanshi. Wai shin wanne irin kirkine da Iyabo, wannan irin kawaici da juriyane da'ita? Hadiza taima kanta tambaya. Kishi na rugurguza zuchiyarta d gangar jikinta. Saita tsinci kanta cikin son zama kamar Iyabo badan komai ba sai dan kishin mijnta da son mantar da Gwadabe Iyabo. Wannan dalilin nata yasa ta cakaloma Ayashe da Sakina zancan Iyabo. Sai dai me da suka soma zana mata Iyabo sai taji e lallai takai macen da dole ta tsaya a zuchiyar ɗa namiji. Sai taji a madadin ta zauna kishin Iyabo ya hanata jituwa da Gwadabe ai gara ta ari rigar Iyabo ta yafa. Amman me a daren ranar Hadiza ko runtsawa takasa yi. Sai jujjuya al'amura take yi a zuchiyarta wata zuchiyar tace da'ita. "Ashe baki cika mace ba in har sai kinyi koyi da halayen tsuhuwar matar mijinki. Kenan ke ba zaki iya juyarma da mijinki hankali ba sai kin zama irin matarshi? Ai kamata yayi kema ki ɓullo mishi da sabon salon tarairaya da tattalin daya doke na beyerabiyar matarshi ba ki tsaya kina bin diddigin halayenta ba" Ai sai ta hau kan shawarar zuchiyarta tayi ɗare_ɗare. Haka dai suka gama kwanakin da zasu yi suka tarkato suka baro Takai da tarin tulin tsarabobin da Sakina da Bara'u sukai musu ƙunshi_ƙunshi. Motarsu tana gudu a hanya. Hadiza zuchiyarta na gudu da tunanin mafitarta itafa tana ji tana gani ba zata bari Gwadabe ya sauya mata ba ta zama itace ma bare ba. Jibi Shafa tun shigowarsu motar take ta janshi da hira ya sake sai amsata yake yi sunata nishaɗinsu. Ajjiyar zuchiya ta sauke haƙiƙa ta fahimci Gwadabe ya gundura da ƙorafinta da saurin fishinta. Ta daɗe tana lura ita Shafa irin matannanne da kamar basu san ciwon kansu ba, kuma ba komai ke ɓata musu raiba. Da ire_iren wannan tunanin bacci yai awon gaba da Hadiza ɗiyarta na rungume a jikinta itama baccin take yi. Juyowa Gwadabe yayi ya kalleta ya lumshe idanu. Hadiza tana da wani matsayi mai girma a zuchiyarshi yana sonta. Sai dai ɗabi'unta na ƙorafi, yawan fishi sun kaishi maƙura shi yasa a wannan karon shima yayi watsi da lamarinta. Ummi ya zare a hannunta hakan yasa ta farka da sauri tare da sake cabke ɗiyarta. "Nine ba wani ba. Kawota ki samu kiyi baccinki" Miƙata tayi ta koma baccinta ba tare da tace dashi komai ba. Sai dare suka isa gidan sosai. Sun jima sosai suna buga ƙofar gidan kafin Mammada yazo ya buɗe musu. "Sannunku da dawowa mutanen najeriya kune da tsohon darennan Gwadabe?" Matan ciki suka yi, Gwadabe ya tsaya suka gaisa da Mammada kafin ya ƙule ɗakin Shafa. Hadiza tana kwance sai juyi take yi fitowarta daga wanka kenan. Tayi tsammanin Gwadabe ko babu komai zai leƙo yai musu sallama ai. Amman sai taji shi shiru a ɗakin Matarshi. Washe gari ma ta jima sosai tana jiran ya shigo su gaisa da taji shirun yayi yawa dole ta goya ummi ta fito ta nufi ɗakin Shafa dan a ƙofar ɗakinta aka jibge tsarabar. "Shafa Gwadabe yana ciki kuwa?" A kitchen ta samu Shafa tana zuba abincin da zata ci. Ita sai lokacin ma ta tuno ashe ko karyawar batai ba. Sai da Shafa ta gaisheta tace. "Da wurwuri ya fita zaije cin kasuwar Damagaram. Ko ya shiga ɗakinki kina bacci ƙila" Wannan abu ya daki Hadiza sosai, sai dariyar yaƙe tayi tace. "Babu mamaki kam dan ban jima da tashi ba. Bari in kunce tsarabar zan shiga ma da su Baba nasu' "To Yaya gasu nan. Nima inna gama karyawa zam shigo cikin gidan " Hadiza dai zuchiyarta na tafasa ta yi cikin gida da tsaraba. Saida ta mikawa matan malam nasu tsarabar kafin ta nufi ɓarayin Baba Fhatsima. "Zafine a garinne Hadiza naga dul kin rame, ga ƙuraje duk sun feso miki?" Cewar Baba Asshi dake duƙe tana dauraya. Baba Suwaiba tace. "Takai fa ƙauyene sosai. Ni nasan ƙauyan da jimawa dole su rame ai" Hadiza dai bata ce komai ba tayi murmushi tasan abune mai wuya ƴan gidan su canja halinsu. Tana shiga ta samu Baba Fhatsima na shan fura. Yaya Tasi'u yana zaune a gefe yana cin ƙwadon zogale." "Hadiza kaddai kune jiya da daddare kuke ta faman dukan ƙyaure?" Cewar Yaya Tasi'u kenan. Murmushin dole tayi mishi tace. "Mune Yaya Tasi'u shigowar dare muka yi. Ina wuni yasu Safara'u, da Anti Badi'a?" "Basa nan sunyi tafiya shekaran jiya suna da biki" "Baba ina kwana mun sameku lafiya?" Abunka da uwa tuni ta gano Hadiza na cikin damuwa ga idanunta sun farfaɗa. "Lafiya lau ya mutanan Takai, inasu Sakina da Toye?" Sai Hadiza ta ɗan sauke kanta sai hawaye shar_shar. Yaya Tasi'u ya miƙe tsaye yace. "Sakara bata da aiki sai shirme. Baba ni zan wuce wajen aiki saina dawo" Baba Fhatsima tace. "To a dawo lafiya. Kar ka manta da maganarmu akan Balaraba kayi tunani ina sauraren amsarka daga yau zuwa gobe" Bayan Yaya Tasi'u ya fice Baba Fhatsima ta mayar da hankalinta akan Hadiza. "Wani abunne ya faru a Takai ɗin. Ko ke da mijinkinne, ko kuma abokiyar zaman taki ce? Ki nutsu kiyi mun bayani" Cikin shessheƙa Hadiza tace. "Baba Tunda muka shiga Takai Gwadabe yaga Shafa da ɗanta shikenan ni da Ummi ya juya mana baya. Sai fishi yake yi, kuma fa har gidan tsohuwar Matarshi a Kano saida abokinshi ya rakashi suka je. Ni fifikon da yake nuna mun ya isheni" Baba Fhatsima tayi shiru cikin karantar yanayinta tace. "Hmm Hadiza ho. Wallahi in kika yi saken da Gwadabe yaga wallanki to wallahi kin shiga uku zaman bazai miki daɗi ba. Hala kin isheshi da ƙorafine, ko kuma wata damuwar ke damun ranshi har kika ga ya canja. Ko kin tambayeshi dalilin canjin nashi?" Hadiza ta girgiza kai halamar a'a" "Kinji irin shashancin naku ai yaran yanzu. Yanke hukunci ba naku bane, zaunar da miji zakiyi cikin kulawa da nuna damuwa da sannu saiya warware miki cikinshi. Da haka mace take zama sirrin mijinta abokiyar shawararshi. In kikayi sake Shafa ta samu wannan kambun bake ba. To abubbuwa da dama zasuita faruwa da mijinki, ƙalilan daga cikine zaki iya ji. Masu yawan yaci ya birne da abokiyar zamanki. Hadiza namiji wawane, kuma sauƙin sarrafawa garesu Wallahi. Abinda yasa na kira namiji da wawa shine. Shifa kulawa da tarairaya, sai ladabi da biyayya,iya girki, iya kwalliya, tsabta iya ɗauke lalurarsa. Shine fa namijin kuma shine zaman auren. Ana mallakar miji da kissoshi sunfu kala saba'in bari in jero miki kaɗan a cikinsu. Akwai kirsar magana Akwai kirsar tafiya a gaban miji, ko kishiya Akwai kirsar rauni, yawan kuka Akwai ta shagwaba Akwai kirsar nuna ma miji ke kullum bai isarki a shinfiɗa Akwai kirsar shimfiɗa Akwai kirsar sa sutura Akwai kirsar iya girki Akwai kirsar ciyar da miji abinci a baki Akwai kirsar yima miji wanka Kirsoshin suna da yawa, ko wanne guda ɗaya kika ɗauka zaki zama ta daban. Kuma zaki zauna daram a zuchiyar mijinki. Shine zakiji yana faɗin alkhairin Allah ya kaima wance. A gaban matarshi zai iya yabon matar data mallakeshi da Tata kirsar namiji ba kunya gareshi ba. Ko kiji yana da wancece da yanzu tayi mun kaza, ko tace kaza. Namiji ya barki da sakakken baki. Su basa raina sauyi, ko jin daɗi duk ƙanƙantarshi. Abubuwa da dama mun ɗauke kanmu akai bamu ɗaukeshi da mahimmanci ba, shigowar boko duk ya wanke muku kanku kun dena biyayya. Mu a zamaninmu a wani gari da Malam ya taɓa kaini muka zauna lokacin sana'ar Malam sai da gishiri da manda ne. To gidan da muke haya akwai wata Fatu bafulatanar Gombe ce. Akan rashin sa ruwa a buta mijinta ya saketa sai garinsu ta koma. To wani akan shara zai iya rabuwa da mace. Wani duk waɗannan ƙanunun abubbuwan harma da manyan bai dameshi ba babu ruwanshi. Amman kinsan babban abinda maza suka wasa shine tsananin kishi, zargi, ƙorafi, bin diddiginsu dan ganin laifinsu, ƙazanta. Waɗannan abubuwan dana jero duk halinki ne banda ƙazantar shi yai silar mutuwar aurenki na fari. Ke ba zaki zama mai kawaiciba, ki gani ƙiri_ƙiri ki nuna baki gani ba. Kiji ki toshe kunnenki. Dole sai anayi ana haɗawa da halin ko in kula, koda hakan zai dameki. Hadiza ki kiyaye abinda zai maisheki bora, Gwadabe fa yana haƙuri dake" Hadiza taci kukanta mai isarta. Baba Fhatsima batai yunƙurin hanata ba har saida tai shiru dan kanta kana tace. "Sai ki kiyaye. In ranar kwananki ya zago saiki bashi haƙuri a bisa kusakuranki da kinfi kowa saninsu. Kuma cikin lallami ki doki cikinshi ya baki labarin matsalarshi. Ke kuma saiki magance mishi damuwar. Inta adda'ace kice zaki taya shi da adda'a. In kuma na shawarane ki bashi shawara, inma na nasihane ki mishi. To zaki ga ko farin cikin ya shiga kece ta farko. Ke namiji sauƙin kai gareshi in baki kwaɓeshi ba sai kiga har asirin kishiyarki ya fasa miki shi babu ruwanshi. Tashi ki koma ɓarayinku" Sallamar Shafa ce ta katse musu hirarsu. Baba Fhatsima ma ce ta amsa mata ta shigo suka gaggaisa. "Malam baya nanne Baba? Shafa ta tambaya" "Bayanan sun tafi taron biki cikin Zinder sai da yamma zai dawo. Ya kika baro mutun Takai dana Habuja?" Murmushi Shafa tayi tace. "Duk suna lafiya Baba. Ga wannan turmin zanine wana yace in kawo miki" Ta miƙa ma Baba wannan turmin zani holan. Baba Fhatsima taita godiya. Anan dai ta tafi ta bar Hadiza dan saida taci ragowar zogalen da Yaya Tasi'u yaci ya rage, ta kora da fura kana ta tafi. Tana komawa gidan ta samu suna abinda suka saba. Wannan karon da matar Mammada da matar Sabitu ne. Dan kaf gidan bada wanda matar Sabitu batai faɗaba shima ɗaure mata baya yake yi inya dawo ta faɗa mishi ƙarya da gaskiya saiya fito tsakar gida da gajeren wando bako riga yaita fitsara. Har Hadiza ta wuce ganin da matar wanta ake rikicin saita tanka. "Haba matar Mammada wannan ai ba halinki bane kiyi haƙuri ki rabu da'ita sharrinta zai koma kanta" Tsautsayi da ba'a saka mishi rana. Buɗar bakin matar Sabitu sai tace. "Ai sharri a jininku yake yawo. Tunda mahaifiyarki ta kakame komai gani take ku kaɗaine ƴaƴa. Kamar yadda Mammada ke da gado, haka Sabitu yake dashi shima. Ina ruwanki da wannan faɗan?" Hadiza tayi kasaƙe tana jin ikon Allah ga Shafa tana tsaye tana jin duk abinda ke faruwa. Hadiza tana juyowa ta cukume rigar Matar Sabitu dambe saiya kaure. To Hadiza ƙaƙƙarface sosai, nan ta guggurje bakin matar Sabitu. Duk da itama ta taɓuka tunda ta gwara kan Hadiza da bango har saida wajen ya fashe. "Shegiya mai haƙoran mayu" A guje Hadiza ta bita Shafa tayi carab ita da matar Auwala suka riƙeta To dama Hadiza kunga a cikin yanayin da dama take wuni tayi tana zage_zage da mita a tsakar gida, tana faɗin. "Daidai nake da ko wacce shegiya a cikin gidannan " matar Sabitu ta leƙo tace. "Harma kina da bakin magana ke da saida aka roƙi Gwadabe ya taimaka ya aureki. Shi yasa aka haɗa auren da Shafa dan itace zaɓin ranshi. Wooo anji kunya anyi bandaro an kasa auruwa" Hadiza sai da tayi ɗan daka ce bata kula matar Sabitu ba, dan ta ɓarar mata da gari a gaban kishiya. Tunda ta shige ɗaki shikenan tayi ƙus. Shafa kuma tayi dariya ta shige ɗakinta itama. To ko da daddare da Gwadabe ya dawo bai fa leƙo Hadiza ba. Tsarabar lemu da ayaba da balangu ya aiko Shafa ta kawo mata. Tana zaune sai jujjuya maganar matar Sabitu take. Gani take kamar gaskiya ne abinda ta faɗa akan aurenta da Gwadabe Fitar Shafa ba daɗewa sai ga Sabitu ya buɗe labulen Hadiza rai a ɓace harda bulala fa. Batai tsammaniba ya shigo ya soma carbaɗa mata. Gwadabe yana cin abinci ya jiyo karan tabka da ihun Hadiza ba shiri ya fito a fusace. Ganin yadda bil haƙƙi Sabitu ke dukan Hadiza Gwadabe yayi kukan kura ya dira a wuyanshi. To gaskiya Gwadabe ba ma'abocin faɗa bane, kuma ko a sifa Sabitu ya fishi jikin ƙarfi zuga Gwadabe yayi da ƙasa yaje ya shure jeren kwallayen Hadiza duk murafen suka rikito mishi. Wannan ƙaran ɓarin kwanukanne ya fito da su Mammada. Auwala ya tari Sabitu ya dinga aika mishi naushi Babu shiri Sabitu ya fito a ɗakin Hadiza da gudu. Ya bangaji Yaya Tasi'u da shima hayaniyar ce ta fito dashi suka faɗi tim a ƙasa tare. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (10) Iyabo:. Duk da ba lafiya ishasshiya gareni ba bada kai nayi bori yahau. Muka raya wannan dare cike da aminci. Washe gari zuchiyoyinmu wasai kamar ma ba mu ba. Bayan Yaya Hamma ya karya yana shirye tsab yace. "Bari inje wajen Baɗejo in karɓo kuɗinn da nace zan biyaki na kayanki da kuɗaɗenki da aka sace. Sai dai baki faɗa mun nawa ne kuɗin ba. Shagwaɓe mishi na kuma yi tunda na fahimci shagwaɓe na daga cikin abinda ke kunna shi. Fuskata ya shafa yace. "Anya yau zan iya fita aikin ma kuwa ba zama zanyi inyi jinyar matata ba?" Da naji ya faɗi haka saina sake matseshi a jikin kujera na soma mishi wasannin da baisan dasu ba sai haɗuwata dashi. Nan muka sake lulawa duniyar ma'aurata. A wannan ranar dai Yaya Hamma saida na roƙeshi ya yarda ya fita. Bayan ya caskemun kuɗin kayana da kuɗin da aka haɗa aka sace mun. Ya ƙaramun da Nera dubu ɗari da hamsin. Ya ƙwaɓeni sosai akan ka da in sake kowa yasan labarin kuɗin daya bani, dan Saniya ƙatuwa ya siyar ya bani kuɗin dukka. Naita mishi godiya na rakashi har ƙofar gida. A tsakar gida naci karo da Uwani. "Uhm Tattabara Uwar soyayya har an shirya da halama komai ya dawo kan seti kenan?" Hannunta naja muka koma ɗakina na danƙa mata wannan kuɗi a leda na labarta mata yadda muka yi ya bani kuɗin. "Kin kyauta ko babu komai kaɗan zaki cika ki ɗakko dila kasuwancinki yaci gaba. Wannan karon me zaki saro to?" To ina ganin kayan yara ma sun wadatar na maza da mata. Tunda ya farfaɗo mun da jarin kinga Shikenan. Uwani tace. "Akwai dubu talatin ɗinki a hannuna kuɗin hayar gidanki du ɗakuna ukun an zuba haya. Kinga bama saina ara miki ko sisi ba. Dana koma Kano zan kira Faty muyi magana, zanje hajj kam in tura mata kuɗin. In kayan sun iso zaki ganni ni da kaina zanzo in kawo miki. Amman Iyabo me zai hana ki shiga ɗakin Hama ki dubo turamen zannuwanki ki kwashe. Mitsiyaciyar dai nasan da kuɗin zata tafi rugarsu" A_a Uwani tunda dai Yaya Hamma ya biyani kuɗin komai harda ƙari bana son in kunno wata fitinar" "Bari kiji Iyabo gobe zata iya miki satar da ta fi wannan muni, sai kiyi yaya kenan in tun yanzu baki ma tubka hanci ba?" Nisawa nayi nace. Idan ta kuma zata gane kurenta kinsan Allah inna zauneta saita amayar da ƴan hanjinta." Nan muka taɓa hirarmu ta yaushe gamo, saida Yafendon tazo tayi mun ya jiki sannan na tuno da ciwo ashe nake. Da safe dai nasha magani, Yaya Hamma ya ɗigamun na idanun yana ta faman yi mun sannu ni kuma inata langwaɓewa. Da yamma na sa mayafina muka je gidan Dada ni da Uwani. Hmm kunsan ƙauye da gulma ashe Dada ta riga da tasan duk abinda akayi sarai, bata shiga zancan bane sabida tasan Yafendo ba zata bari a cutar dani ba, haka shi kanshi Hamman bazai cutar dani yana cikin hayyacinshi ba. Nasiha da ban haƙuri ta dinga yi mun, tare da jajanta mun bisa asarar data hauni. Da yamma sakaliya muka koma gida muka tarar ƙanwar mahaifiyar Hama tazo an turota jin ba'asi. Su Baɗɗo suna tsakar gida suna aikace_aikacensu muka wuce, matan gida kuwa in banda Safiya babu wacce taimun ƙaƙa jiki, mazajensu dai sunzo sun dubani, amman dake su a bayan Hama suke shi yasa haushina ma sukeyi. Washe gari sassafe Uwani ta kama hanyar Kano. Wannan karonma ta sari man shanu a hannun Baɗɗo mai yawan gaske. Gaga_gaga soyayyarmu ni da Yaya Hamma ta ƙara burunƙasa matsawar da Hama tayi saita bamu damar sake shaƙuwa da junanmu, mukaita ragargazar amarci. Yaranta kuwa a cikin kwana biyar da tafiyar uwarsu harsun sauya. Na tsefe musu kansu na wanke musu tas, na musu kitso, kullum saina musu wanki tare da Babansu da Yafendo. Gari ya ɗauka amaryar da Hamma ya auro a birni ta mallakeshi ta rabashi da Matarshi. Shima har tareshi akeyi a hanya ana mishi magana akan ya daure ya dawo da Hama. Abu ɗaya yake faɗa musu Yafendo ce ta koreta ba shiba, bashi da damar tsallake maganar mahaifiyarshi. Ni dai a cikin sati biyu da tafiyar Hama har wani haske da ƙiba nayi, kullum Yaya Hamma sai ya riƙo mun kayan daɗi yake shigowa, ga wani irin tattalina da yake yi. Roƙonshi nayi akan inaso in soma koya ma Baɗɗo da Safiya karatun Qur'ani a tsakankanin magriba zuwa isha. Babu musu ya amince mun nake koyar dasu a tsakar gida. Abu kamar wasa ba sai har matan maƙota suka soma shigowa ɗaukar karatu ba. Ya zamana ina koyar da mata ashirin karatun Alkur'ani da kuma abinda ya danganci tsarki, da alwala. Abun mamaki da yawansu basu iya wankan tsarki ba, ƙalilan daga cikinsune suka iya sai gyara da akayi musu. Ina jin daɗin ɗalibaina suma suna jin daɗina. Wannan makarantar daren saita sake debe mun kewa, ya zamana kuma an sanni sosai a ƙauyan. Wata ranar juma'a da rana babu kowa a gidan ina kwance ina karanta littafin Hausa mai suna Allurar cikin ruwa na Bilkisu funtua . Bayan na gama bitar fassaran hadisin da zamu yi da ɗalibaina. sai kawai naga an wangale mun labude. Ɗagowar da zanyi sai naga Hama ce riƙe da labulen. Duk ta rame idanunta ya zurma. "Kinci nasara a kaina gaki ga gidan Hamma. Ni zan bar miki gidan baki ɗaya kayana nazo kwasa. Amman ki sani babu ke babu kwanciyar hankali sai kin fita tsirara a haukace daga ruggarnan" Ta saki labulen tana wata dariya. Jikina sai naji ya mutu murus na rasa kataɓus. In yinƙura in tashi na kasa, inaji Hama nata kwaramniya a tsakar gida. Ashe kayanta ta kwashe tsab saida Yafendo ta dawo muka gani, ko tsinke Hama bata bari ba. Da Hamma ya dawo da daddare ya sameni a ɗakin Yafendo ta labarta mishi hama ta kwashe kayanta. Duk saiya shiga damuwa ainun ina lure dashi. Ko da muka koma ɗaki kasa cin abinci ma yayi, ƴar hirar da muka saba ma yau babu. Yaya me zai hana kaje kayo bikon matarka ta dawo tunda kana son matarka ga yara a tsakaninku" Anan naji abinda ke cikinshi. Cemun yayi. "To ya zanyi Dada taƙi fur. Kullum inna shiga saina roƙeta akan tayi haƙuri ta yafe ma Hama ta dawo ɗakinta ko dan sabida yara, maganar gaskiya nima inason ta dawo. Sai tace a'a" Shiru nayi ina kallonshi da mamaki bil haƙƙi a cikin damuwa yake. Saina sanya salama a zuchiyata nasan lafiya lau yake zaune da matarshi kafin zuwana, har tatsar nono tare suke yi, tare suke duba dabbobi marasa lafiya. Bazanyi tsammanin ya soni fiye da Hama ba. Miƙewa nayi zuruf. Yayi saurin kamo hannuna muka ƙurama juna idanu, kishin sai neman ingizani yake yi, nifa sai naji nama tsaneshi ni kam, kamar in dira a wuyanshi haka nake ji. Ina zuwa yanzu zan dawo" Na furta a raunace. Idanu ya lumshe ya miƙe tsaye ya shige jikina ya ƙanƙame ƙuguna ƙam. Runtse idanu nayi kawai kishi nata ɗawainiya dani, sha'anin maza akwai munafurci a ciki. Babu mamaki acan ɗakin Haman haka yake mata irin wannan soyayyar koma fin hakan. Ai da wannan tunanin ya bijiro mun saina sa hannu bibbiyu na ɓamɓareshi a jikina na fice, inaji yanata kiran sunana ko tankashi bamba. Ɗakin Yafendo na shiga har tayi shirin bacci. "Jabu lafiya kuwa" Tsugunnawa nayi nafi minti talatin ina bata baki akan ta yi haƙuri Hamma ya dawo da matarshi. Ta dinga kwatantamun in bari kawai tunda Hama da kanta ta yanke hukuncin haƙura da shi. Na kafe akan ta dai yi haƙuri. "Shikenan Jabu jeki Allah yayi miki albarka" Ameen Yafendo nagode, sai da safe" Sallama nayi mata na fita. Ina zuwa daidai bakin ƙofar ɗakina sai naji kamar wani abu ya shiga jikina haka. Nayi saurin runtse idanuna ina karanto duk adda'ar da tazo bakina, har saida na samu nutsuwa. A sanyaye na shiga ɗakin inaji tsigar jikina na tashi. A kan gado ɗare_ɗare na samu Yaya Hamma idanunshi biyu amman ya shiga zurfin tunani juyo kai yayi muka haɗa idanu. Hannuwanshi biyu ya miƙo mun halamar inzo in shiga jikinshi. Basarwa nayi na samu jefen gado na zauna. Hannayena duka biyu Yaya Hamma ya riƙo yana murzasu yana daga kwance, suna ratsani sosai. Da wata murya sassanya yace. "Ina kikaje kika barni ni kaɗai cikin kewa" Idanuna na lumshe a zuchiyata nace. Lallai kishi aikine ja, banga laifin Hama ba da taita hauka lokacin da za'a auroni. Bansan sanda nace. Kewar uwar ƴaƴanka data bar gidanka ko?" Da sauri ya miƙe zaune banyi aune ba ya soma aiko mun da saƙon kai tsaye, tun ina gane yaren har na dena gane komai ya fahimci raina ya ɓacine da damuwar daya nuna akan matarshi a gabana, sai ya zage ya dinga mun abubuwan da yasan inaso sosai. Sai da komai ya lafa kishin yaci gaba da nuƙurƙusata. Shi fa gogan yama yi baccinshi niko idanuna biyu ina kallon hawa da saukan numfashinshi. Ina aiyanawa a raina, ko wanne irin kalami yake ma Hama oho, gashi ya iya soyayya mai sanyi da tsaiwa a rai. Nina ɗauka irin wannan soyayya sai mutanen birni, ashe abun baiwane daga Allah. Sannan ya danganta da yadda namiji yake son mace. Su fulani Allah yayi su da iya soyayya da son mace sosai. Sai Allah ya basu basirar iya tattalin macen gashi dai rayuwarsu a ƙauye, mazan kuma rabin rayuwar a jeji ma suke yi. Wannan dalilin yasa matan fulani sunansu yai shura wajen kishi da yima kishiya mugun asiri. Ajjiyar zuchiya nayi na shafi fuskar ɗan fulanina ina murmushi. A haka bacci ya kwasheni. Amma me zai faru ina cikin bacci sai naji kamar ana tsaye a kaina. A razane na tashi zaune dafe da ƙirjina, hakan yasa Yaya Hamma ya tashi shima, yana riƙe dani ni kuma na runtse idanuna Wannan inuwar tana saitina. A zahiri ina ganin inuwa, a cikin jikina kuma ina jin halamar mutum a tsaye a kaina. Yaya Hamma yana tambayata menene, ni dai adda'a nake yi babu ƙakƙautawa da ƙyar na buɗe idanuna sai naga wayam babu wannan inuwar. Ajjiyar zuchiya na sauke na kwantar da kaina akan ƙirjinshi. Hannu yasa yana shafar bayana mai cike da tsoka yana mun raɗa a kunnena. "Menene ya tsoratamun ke Jabu, mafarki mummuna kikayi?" Ni dai sai ajjiyar zuchiya nake saukewa, a hankali ya kwantar dani yana shafar kaina. Ni dai harya koma baccinshi , idanuna biyu. Dana rufe idanu sai wannan inuwar ta dawo, dana runtse idanu nayi adda'a inna buɗe sai inga babu, gashi babu tsarki a jikina ƙaƙa_sara_ƙaƙa. Babu damar yin sallah. Adda'a inna kamo wannan sai in faɗa waccan cikina ya duri ruwa sosai da sosai. Daren yayi tsayi kafin garin ya waye. Ko da na shiga bayan gida yin wankan sallah ina tsaka da yin wankan sai naji kaina na juyawa tsigar jikina na tashi. A lokacin ji nake yi kamar in fito tsirara dan tsoro da firgici. Da ƙyar da ɓarin jiki na gama wankan, na fito na tarar Yaya Hamma ya tafi masallaci. Ina ganin ɗakina amma wallahi na kasa ɗaga ƙafata in shiga. Dana gaji da tsaiwa da ɗaurin ƙirjin kamar mahaukaciya sai gani a ɗakin Baɗɗo. Ko ita data ganni saida ta tsorata. "Adda lafiya kika fito haka, ko wani abun ya sake haɗaki da Yaya Hamma ne?" Sai naji hawaye na zuba a idanuna. Babu komai ke dai jeki ɗakina maza ki ɗakkomun kayana in saka zanyi Sallah " Baɗɗo tayi maza taje ta ɗebo mun kayan nawa nasa nayi Sallah a ɗakinta. To a gaskiya a wannan lokacin nayi sallar ne, amman bana ce ga abinda na karanta ba. Inyi adda'a na kasa sai naji zuchiyata tayi wani irin mugun cunkushewa. Sai kawai na saki kuka. Baɗdo na shirin fita na kirayi sunanta. Karki kira Yafendo, ki riƙe mun sirrina Baɗɗo. Ke dai ki taya ni da adda'a dan auren ya isheni ya fice mun aka zaman ƙauyannan." Shiru tayi kamar ruwa ya cinyeta. Ni kuma sai kuka kawai nake rerawa a haka Yuguda ya shigo ya iskemu. Ya tambayi Baɗɗo wani abun ya sake faruwa ne. To itama ba sani tayi ba, juyawa yayi sai gashi ya dawo tare da Yaya Hamma, sai suka fita suka bamu waje, suna fita na faɗa jikinshi na ƙara fashewa da kuka. Ƙanƙameni yayi wallahi ina jiyo dukan da zuchiyarshi take yi, jikinshi har rawa yake yi. Ya kasa cemun komai bai hanani kukan ba, sai bayana yake shafawa. Da yaga bani da niyyar yin shirune ya ɗagoni muka haɗa idanu idanunshi sun zama kamar gaushi, fuskarshi ta dawo kalar tausayi, ga soyayya muraratan ina karantawa a idanunshi, fuskarshi, dama gangar jikinshi. Muryarshi a dakushe yace. "Menene ya faru, me akayi miki kike kuka haka, bakya jin tausayinane, ko dan kinga bana son kukanki ne shi yasa kikeyi dan ki horani?" Idanu ya lumshe ya buɗe su a kaina. Yaya Hamma wallahi ina sonka, Allah ya gani inason zama dakai, ina son ƙare rayuwata dakai. Amma....." Da ƙarfi ya mayar da kaina ƙirjinshi numfashinshi yana hawa da sauka. Banyi aune ba ya ɗagoni ya zura bakinshi a cikin nawa, tsabar ina sonshi haka na dinga shan wannan yawun mai ɗan bashi, dukda yana goge bakinshi kafin yaje masallaci. Ni ko goge bakin nawa banyi ba. Mun daɗe a haka kafin ya dubeni, nima shi nake kallo sonshi na sake ninka kanshi a zuchiyata. "Mu tafi ɗakinmu Kar muyi abun kunya a ɗakin ƙanne" Ba musu na bi bayanshi. A ɗakin Yafendo muka yada zango muka gaisheta. "Dada yau batai ɗumamen safe ba, jiya mun kwana bata jin daɗi. Amman zata ba Baɗɗo ta dumama kafin Amaduyal yazo ɗaukar abincin Dada" Kaina na sunne. Yafendo tace. "Ayya sannu Jabu Allah ya ƙara sauƙi" Kaina na ƙasa na amsa mata da ameen. A wajen na sulale na fito na barshi. Baɗɗo har ta shiga ɗakina ta fito da ɗumamen ma. Tana tsaye da Amaduyal suna tattaunawa na isa wajen ina ƙaƙaro fara'a. Me ake tattaunawa ne Amaduyal?" Dariya yayi yace. "Adda jiya da daddarene Yusufu yazo yake faɗama Dada wai yau za'a ɗaura auren Cubu. Ya bada aurenta ma abokinshi Baffa Modibbo" Idanu na zare. Abokin Baffan naku akaba Cubu yarinya karama da'ita. Ita za'a ba tsoho?' Baɗɗo tace ." "Hmm ai tunda Baffa ya faɗa babu makawa. Damma Baffa Modibbo dattijon arzikine. Sai dai Hajaru ƴarshi aminiyar Cubu ce, tare suke zama a wajen saida Nono." Shiru nayi lamarin duk yabi ya dameni ya addabeni. Ga matsalar data tunkaroni, ga kuma wannan matsalar. Ajjiyar zuchiya na sauke. Dada me tace da taji wannan labarin? Na tambayeshi. "Babu abinda tace face fatan alkhairi. Ai aurenta yafi zaman gidan. Dan ke bakya zuwa gidanne da in kika ga irin rayuwar da sukeyi sai kinyi musu kuka. Gidan Baffa Modibbo kuma abinci me kyau suke ci. Kuma matanshi basa tallar Nono yana da yawan shanaye, kuma sha'awar haɗa iri dasu akeyi." Shiru nayi ina hango cutarwar da hakan zai haifar. Amman yana iya, babu har sai naji ta bakin manya, duk da suma da halama babu abunda zasu iya. Ɗan daɗin da naji mata bai wuce na barin hannun matan ubaba, da kuma samun ƴanci daga gantalin zuwa tallar nononnan. Ita kanta Baɗɗo da sannu zan hanata wannan tallar nono, ta kama sana'ar yi. In kasuwancinta na man shanu ya kankama da Uwani shima zai rage wani abun. Dan Uwani tace ta dinga soyawa tana tara mata ko na nawa ne in tazo, ko inni zanje a tafi mata dashi. Amaduyal yace. "Dama Yafendo nazo faɗama. Baffa Musa yace mu je duka mu sameshi a gida har daku. Bari inje wajen Yafendo" Ya tafi ya barmu. Na dubi Baɗɗo nace. Kar ki faɗama kowa halin dana shiga Baɗɗo. Babu kuma abinda Yaya Hamma yayi mun ke dai ki tayani da adda'a kawai" Murmushin jin daɗi tayi tace. "To Shikenan Adda, Bari in ɗunduma tuwo in kawo muku naku" To Kawai nace, na wuce. Ina zuwa ƙofar ɗakina ai sai na doge, tsigar kaina taci gaba da tashi. In shiga na kasa tsoro nake ji. A wajen Yaya Hamma ya sameni. Hannuna ya riƙe muka shiga bayan nace. A'uzubillahi minal shaiɗanun rajim. Ina sauke ɗayar ƙafar a cikin ɗakin sai naji abu ya kuma shiga jikina. Take sai ɗakin ya shiga jujjuyamun. luuu nayi na tafi zan faɗi, Yaya Hamma ya taroni, amma tare dashi muka faɗa kan kujerar nayi mishi nauyi bazai iya taroni ba. A zabure ya miƙe yana jijjigani. Ni kuma na kasa buɗe idanuna dan ɗakin jujuyawa yake yi dani. Adda'a kawai nake yi ina girgiza kai ina hawaye. Nafi minti goma a wani hali wanda bazan iya fassarawa ba da ƙyar na dawo daidai. Na faɗa ƙirjinshi ina kuka. Ni Allah bazan zauna a ɗakinnan ba sai dai ka canja mun ɗaki. Ko kuma in tafi Kano" Kanshi kawai ya ɗaga sama yama rasa me zaice. Sallamar Baɗɗo ne yasa ya sakeni ya tashi. Tiran hannunta ya karɓa ya shigo dashi. "Sakko ki karya. Sai in kaiki gidan Dada ki zauna. Inna dawo aiki zan biya in ɗaukoki hakan yayi miki Jabuna kafin mu nemi mafita?" Kai na gyaɗa mishi halamar yayi mun. Hakan kuwa akayi muna gama cin abincin muka fito tare, ya bani dubu ɗaya yace in yi girki acan in naje muci Yafendo bata nan ma ta tafi kiran Baffa musa, Baɗɗo ke faɗa mana. Saina dubeshi nace. To kaje aikinka zamu je gidan Baffa Musa ni da Baɗɗo. Zan tafi da yaran sai mu wuni acan gidan Dada" murmushi yayi mun yace. "To Shikenan. Ki kula dan Allah. Saina dawo, ku gaishe da Baffa Musan. Amman me akeyi acan gidan nashi da ni ban sani ba?" Baddo sai ta bamu waje, ta haɗa kan yaran suka fita. Ni kuma na labarta mishi abinda ake ciki da ƙin auren da nakeyi sabida hakan ka iya cutar da lafiyar Cubu. Shi kuma ya nuna mun ai babu komai kuma ba'a kanta aka soma ba, kuma gidan da zata shiga gidane mai daraja gidan arziki. A haka dai mukai sallama shi ya tafi aiki, mu kuma muka nufi gidan Baffa Musa. Acan tattaunawa kawai akayi akan gudunmawar da zamu haɗa, bawai akan auren dole da tsoho da za'ayi mata ba. To kayayyakin ɗakina da sukai saura suna gidan Dada nasa an ajjiye mata harda kujera 1_1. Na ware mata dogayen riguna da zanin gado har kala uku masu kyau, ta samu kular zuba abinci mai tsada da tire harda plate da tsokali. Ni duk wata gudunmawata na ajjiyeta tuni. Nan muka gama tattaunawa mukai ma Baffa Musa sallama muka tawo gidan Dada harda su Yafendo A'i. Daga nan suka shirya dan zuwa gidansu Cubu, amman ni ban dani, ni sai zuwa gobe in an kaita ɗakinta sai inje ayi yinin biki dani. Bodi ( keken shanu) suka tafi da kayan zuwa can gidan Mai Nagge. Ni da yarana kuma mu kai zamanmu a wajen Dada. Wankinta na tattaro na fito dashi tsakar gida, na soma wankewa. Mai sunan Yafendo kuma na kirata na aiketa siyo kayan miya da garin tuwo. Ina gama wankin Dada na shiga aikin kwalime mata ɗaki, ga miyar kuka harna kaɗa na maida ruwan tuwo. "Jabu sai yaushe kayanki zasu zo ne, maƙota suna yawan shigowa neman kaya sai dai Kari tace musu kayan suna hanya" Ninkin kayan na ɗan dakatar nace. Dada suna hanya. Da zaran sun iso zaki ga Uwani zata kawo mun. Gobe ma inaso zan shiga gari gidan matar ogan Yaya Hamma in dubosu. Zan kira Uwanin a waya muji." Kai kawai Dada ta gyaɗa mun. Na ci gaba da aikina sai da mukayi sallar muka zuba tuwo da zafinshi muka ci muka ƙoshi dam. Dama har dare nayi tuwon dan inna koma gida bazan yi girki ba. Tsiren da ya zamema Yaya Hamma jiki wajen siyo mun, shi zanci in sha tea abuna. Ƴan biki sai magriba suka dawo niƙi_niƙi da tuwon biki an kawo ma Dada nata. Yafendo A'i tace. "Jabu har yanzu baki tafi gidanki ba?" Murmushi nayi mata nace. Yace in ya dawo zai biyo mu tafi. Sannunku da dawowa" Suka shiga ciki. Baɗɗo ta tsaya a wajena tace. "Adda dama a wajen bikine adda Daso take faɗan wai Hama ta kusa dawowa. Kuma kullum sai Yaya Hamma yaje wajenta. Yanzu haka ma tace ba zata dawo ba saiya sake mata kayan ɗakinta kab. Sai garashi take yi sunata cin kuɗinshi" Jim nayi ina nazarin maganganun Baɗɗo. Kullum sai yaje wajen Hama? Maza mutananmu kenan. A zahiri nace. "Ita Dason dawa take wannan hirar?" "Da Sadiyan Yafendo A'i suke hira. Har tana faɗa mata wai hatta dukan Hama da Adda Uwani tayi ashe sai da Yaya Hamma ya ba Hama dubu goma wai kuɗin magani" Ajjiyar zuchiya na sauke nace. Hmm wannan a wajen namiji ba komai bane Baɗɗo. Babu komai. Ina mamakin yadda Daso ƙiri_ƙiri ta zama maƙiyiyata akan kawai Yaya Hamma." Zuwa bayan Isha su Baɗɗo duk suka watse bayan sunci tuwon biki, yaran ma Yafendo ta kama hannunsu suka tafi tare Tuwon da nayi ma sai dai su Dada su ci da safe dan ko buɗeshi ba ai ba, sun samu na gidan biki mai nama. Ni dai ina tsakar gida jigum nayi zurfi a cikin tuntuntuni sai ga sallamar Yaya Hamma. Ɗagowa nayi na kalleshi, shima ni ɗin yake kallo. Sai wani murmushi yake yi mun. Ni kuwa haushi murmushin ya ƙaramun. Sannu da zuwa" Iyakar abinda na ce dashi kenan. Sai ya sha jinin jikinshi, ya fuskanci raina a ɓace yake. "Dada fa?" Tana ciki, yanzu ta shiga" Sai ya kutsa kai cikin ɗakin. Ya daɗe a ciki kafin ya fito yace in taso muje. Sallama nayi musu na bishi muka tafi. Tun fa a hanya yake magiyar in faɗa mishi menene ya ɓata mun rai. Amman amsa ɗaya nake bashi cewar babu komai. A haka har muka iso gidan. Matan gidan suna tsakar gida, tare da matan maƙota da nake ma karatu. Suna ganina suka soma murnar ganina. Haƙuri na basu akan sui haƙuri sai gobe zamu yi karatu, duk na sallamesu suka tafi gidajensu. A ɗakin Yafendo na samu Yaya Hamma tana mishi maganar Hama. Da naji haka saina gaisheta na fice abina na jirashi a ƙofar lungunmu harya iso muka shiga. Ina shiga ɗakin sai gabana ya yanke ya faɗi haka. Cikin dauriya muka sha tea da balangu da masa dai mu kai shirin kwanciya. Baccin da bai yiwu ba kenan fa. Irin na daren jiya sai abinda ya ƙaru dan ɗakin har jijjiga naji yanayi ƙasa na zubowa. Wannan yanayi sai ya zame mun jiki, ni da bacci sai na rana, kuma sai dai in wuni a tsakar gida ko wajen Yafendo dai. Mu'amalar aure ba sai ta gagara ba. Sai mun haɗu zuwa gobe kuma✍🏻 Mrs Bukhari ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (11) IYABO:. _Assalamu Alaikum barkanmu dai mata ƴan uwana_ _Masu yawan damuna akan in buɗe group na musamman na kasuwanci, baƙi nayi ba abubbuwanne sai godiya.__amman naji ƙorafe_ƙorafenku zan buɗe kafin in kammala wannan littafin_ _duk mai son ganin kayana da kuma farashin nawa nake saida ɗaiɗai da sari duk zaku dinga gani da izinin Allah nagode nagode)_ Ba sai ina tare da nutsuwa bane har zamu iya mu'amalar aure ba? Banfa mance da furucin Hama ba yananan daram a raina. Ban ɗauka zata iya mun komai ba face abinda yazo a zanen ƙaddarata shi yasa. Haka dai nake ta gurgura rayuwar watana guda cur a cikin wannan yanayi marar daɗi. Amman in fa gari ya waye na baro ɗakin Shikenan zanci gaba da harkokina. Ga ɗalibaina da suketa ƙara yawa yanzu harda ƴan mata. Ganin sunyi yawa saina sanya musu nera ashirin ashirin duk sati kuɗin laraba. Daga koyarwa ba saina soma buɗe musu karatun yadda zasu kula da kansu ba? Karatu kunga ai ya ƙara armashi. Ranar dana koma asibiti karɓar maganin ciwon ido, wanda duk wata ba fashi ina zuwa, duk da idonma yanzu ko inuwar bana gani ya riga daya mutu mus wallahi, kuma duk inda Yaya Hamma, ko Yafendo suka ji mai maganin ciwon ido sai sun karɓomun, amman dai ido ya riga daya mutu mus, nace ma bazan sake komawa asibitin ba. Saina kira uwani nace in zata zo ta shiga kurmi ta saromun magungunan mata ta tawo mun dashi, dasu turare ɗan ɗuri, da janbaki, hoda, gazal, kayan dai kwalliya a jimlace, da su yari. Wannan matsalafa tana damuna. Wata ranar talata muna kwance Yaya Hamma yana murƙususu yana buƙatar mace, gashi bansan dalilin rashin tarewar Hama ba. Sai nace dashi ina kuka. Ka taso muje ban ɗaki in biya maka buƙatarka. Ko muje garken Shanu" Kallona yayi sai yayi murmushi. "Ke da kike fama da lalura yaushe zan kai ki banɗaki. Nayi magana da Baɗejo gobe ke da matarshi zaku je gidan magani" Hawayena ya shiga sharemun. Ya ja hannuna muka fita, ina biye dashi sai gamu a ƙofar ɗakin Hama. Yaya Hamma me zamu yi anan?" Ya kalleni da runannun idanunshi wanda suke sani kasala a kunnena yace. "Duminki kawai nake son inji. Ina kewarki fiye da tunani" Idanuna na lumshe a zuchiyata ina roƙon Allah ya kawo mun mafita. Adda'a inayi babu dare babu rana wallahi. A.a ni bazan shigar mata ɗaki ba. Duk da babu kayanta a ciki. Amman ai ɗakinta ne, koni kayi ma haka na samu labari bazanji daɗi ba." Baice dani komai ba ya jani zuwa garken shanunnan. A tsakankanin shanu muka gudanar da soyayyarmu, ina kwance a cikin kashinsu. Kuma ya bani kulawa sosai ga kewar juna dama munayi sosai. Me zai faru, wallahi sai ga bacci. Watana ɗaya da kwana goma cib baccin dare yafi ƙarfina kaina kamar zai buga. Shi kuma jin daɗin nayi bacci yasa sai ya gyaramun kwanciyata, shima yayi kwanciyarshi. Gamu a tsakankanin Shanu suma suna kwance. Kiran sallar assalatu ne ya tashemu. Kunga ya tabbata a cikin ɗakina matsalar take kenan. Gashi Bama son kowa yasan matsalar dake faruwa a tsakaninmu Mu kai wanka, shi ya wuce masallaci ni kuma na wuce garke wajen tatsar madara. Matan gidan duk suma suna wajen ko wacce tana aikin dake gabanta. Sai wani habaici da sokiburutsun zantuka na jahilci da rashin wayewa suke yi. Wanda ya zame musu jiki. Dan ni kam a tsakaninsu dani ko ga miciji bamayi. Haka Baɗɗo ta zama saniyar ware a cikinsu. Suna gani ina koyarwa, amman ɓakin hali da gabar da suke yi dani yasa suna son makarantar, amman ba damar shiga. Gashi sai cika ake kuma yi. Yafendo ma tace a gina mun rumfa sabida lokacin damuna ruwa bazai barmu yin karatunba. Da rana ina tsakar gida ina wanke_wanke sai ga sallamar Uwani. Ga wasu matasa a bayanta ɗauke da dilar kaya. Itama ga jakar kayanta a buhun Kano ta ɗau zafi tanata faman kici_kici. Da sauri na wanke hannuna tsab naje na amshi buhun Kano ta ɗau zafin a hannunta. Yaran kuma na nuna musu ɗakin Baɗɗo a ciki suka sauke mun dilar. Na basu tukuici suka fice suna godiya. Sannu ta balbalin kin shawo rana" "Ke dai bari Iyabo. Ana kwanɗa rana da zafi. Bari mu gaisa da Yafendo tukunna." Ta wuce wajen Yafendo. Ni kuma na shinfiɗa mana tabarma a barandar kofar ɗakin Hama. Na cika mata ruwa da kofin sulba ruwan na randar ƙasa mai sanyi. Na zubo mata jallof ɗin shinkafar manja mai bushasshen kifi. Itace farkon zuba ma, dan yanzu na sauke. Na zuba na Yafendo na miƙa mata, muka fito tare da Uwani. Ga tabarma can a inuwa kije ki zauna kisha ruwa mai sanyi, zan zuba ma yara abinci sai inzo" "Iyabo ko laulayin ciki kikeyi ne, kinga yadda kika zuge kuwa?" Hawayene ya cika gurbin idanuna tab. Da ƙyar na saisaita kaina nace. Tabalbalin akwaiki da wutar ciki. Inma cikinne dani duk zaki ji ai. Ina zuwa" Kitchen na wuce, ita kuma taje ta zauna a wannan shinfiɗa da nayi mata. Ina zuba ma yara abinci saiga matar Baɗejo ta leko. "Malama sannu da aiki. Kin ganni sai yanzu. Wallahi wanki nayi ne shi yasa" Duk ɗalibaina da malama suke kirana. Ɗagowa nayi nace. Ayya babu damuwa. Dan Allah zuwa wajen maganin mu bari bayan la'asar baƙuwa nayi daga Kano. Bari in zuba miki abinci ko yara kya ba suci. Na cika mata ɗan china da shinkafa taita godiya. Suka gaisa da Uwani ta fice. Saida na sallami yaran nazo na zauna a kusa da Uwani " MARAƊI Tare suka faɗi rakwatsam a cikin bokatai. Sabitu yana kan burgujejen tumbin Yaya Tasi'u. Hadiza kuma duk zafin dukan da Sabitu yayi mata bai hanata yima Gwadabe dariyar mugunta ba. Data kalleshi a tsakiyar kwallaye tsamo sai ta kuma tuntsurewa da dariya. Shi kuma kunya duk ta lulluɓeshi ji yake inama ƙasa ta tsage ya faɗa ko ya huta. Haka ya yunƙura ya bi bayan su Auwala ya bar Hadiza a ƙasa tana dariyarshi. Da sauri Sabitu ya ɗaga Yaya Tasi'u. Sai da Mammada ya taimaka ma Yaya Tasi'u kafin ya iya tashi abinka da mai jiki. "Meke faruwa, duk me ya kawo wannan rikicin?" Yaya Tasi'u ya tambaya yana zazzare idanu. Hadiza ce ta fito ta bashi labarin sale_salin rikicin, da zuwa zaneta ta yayi har ɗaki" "Bazan lamunci wannan iskancinba. Rashin darajar matarka yayi yawa da kowa faɗa take yi. Ka sani duk ranar da matarka ta sake takalo rigima irin wannan a gidannan to daga kai har ita ba zaku ji daɗi ba. Akanme kuma zaka bi Hadiza har ɗakinta ka daketa sabida matarka, kuma shima Gwadabe har ka tureshi. Mace na nema ta mayar dakai sususu shashan banza." Nan Yaya Tasi'u yaita ruwan faɗa yana hargagi. "Duk kuje ku kwanta. Banason jin wannan maganar a cikin gida a kiyaye lafiyar malam. Zan saɓama duk wanda ya shigar da labarin gida har yaje kunnen malam. Gwadabe kayi haƙuri. Kema Hadiza kiyi haƙuri, kuma ki kiyaye kinsan Sabitu dashi da matarshi duk ƴan hau ne tuburarrune" Nan Yaya Tasi'u ya kashe kes ɗin, kowa ya shige ɗakinshi. Ko washe gari Gwadabe bai leƙa ɗakin Hadiza ba balle yaga yata kwana, kuma ya gani ko Sabitu yayi mata rauni. Itama da damuwar abu biyu ta kwana. Damuwar rashin haɗin kan gidansu, da damuwar maganganun matar Sabitu. Waɗannan abu biyu su taita tubka a kansu tana warwara. Ta wayi gari da baƙin cikin fishin da Gwadabe yake yi da'ita wanda a yanzu tayi imani Shafa tasan fishi yake yi da'ita. Yau monday dukkansu ficewa wajen aiki suka yi Hadiza na dawowa ta ɗaura farfesun naman kan rago data siyo. Ta jiƙa shinkafar tuwonta dan lafiyayyar masa take so tayi musu suci da romon ganda. Da ɗan dama ta jiƙa shinkafar dan tana son ta miƙa ma Malam shima tasan yana son waina. Sai ta shiga aikin ƙalƙale ɗakinta A zahiri Hadiza irin matannanne da zaku ga komai na ɗakinsu ƙal filin tsakar ɗakinsu sai kaga kamar ba'a takawa. Badai kaga datti, ko ƙura ko ƙasaba. Komai kuma yana zaune a muhallinshi. Shafa na da nata irin tsabtar amman ba irin na Hadiza bane, dan irin su Hadiza har cewa dasu akeyi masu aljanun tsabta, in tsabta tana yawa to tasu tayi yawa ma. Data gama ƙalƙale dakinta ta fito ta shiga gyaran kitchen. Shafa na barandar ɗakinta a zaune tana wasa da Abba sai dariya yake yi. Daga haka sai Hadiza ta jiyo kakarin aman Shafa a bayan gida. Da sauri ta iso ƙofar bayan gidan tana tambayarta me taci, ko dama bata da lafiyane? A galabaice ta fito ta zauna. "Lafiyata ƙalau Yaya, kuma ni banci wani abu da zai tayar mun da zuchiya ba. Tun safe nake jin jikina wani iri haka dai. Sai jiri da nai ta ɗan ji a wajen aiki. Amman inaga gajiyar hanya ce. Shiru Hadiza tayi tana karantar yanayinta. A cikin zuchiyarta tace "Shafa dai ƙarfi da yaji itace uwargidan Gwadabe. Ni dai nawa uwargidan sunane. To mi ya rage, ta haifi ɗa namiji gashi babba. Yanzu daga dawowarmu har Gwadabe ya ɗirka mata wani cikin zata kuma rigani haihuwa, ni shikenan na zama ƴar kallo. A zahiri kuma Hadiza tace. "Bazai wuce gajiyar ba. To Allah ya ƙara sauki. Bara inje gida zan aika almajiran malam sui mun markaɗe inna gama gyaran gidana" Shafa tace. "To sai kin dawo. Ni kam banji duriyar ummi ba tunda kuka dawo ko kukanta ban jiyo ba?" "Ummi iyayen rigima tanata bacci. Yanzu sai dare yayi mu ta hanamu baccin " murmushi kawai Shafa tayi. Hadiza ta ƙarashe gyaran kitchen ta kwanke banɗakinta, ta ɗauro alwala. Sai da tayi salla kana ta fice ta bar ganda akan gawayi a hankali gawayin yake ci babu yawa tasan ƙila ma mutuwa zaiyi nanda ɗan wani lokacin. Hadiza dai harta gama tuyar masarnan tana ta aikin tunani duk ta shiga damuwa. A sanyaye ta miƙa ma matan yayunta masa, tasa mayafi ta kai ma Baba Fhatsima tace ta ba Malam. Zuwa taran dare saiga Gwadabe ya shigo. A lokacin tana tsaye taci kwalliya da riga da wando, ga kanta yasha kitso. Ummi na bayanta tana jijjigata sai ƙananan kuka take yi. "Sannu da zuwa" Ta faɗa tare da karɓar ledojin hannunshi ta ajjiye a gefe. Akan daddumar data jera kulolin abinci da duk abun buƙata ya zauna. "Yauwa. Meya sameta ta hanaki zama" dukkansu babu yabo babu fallasa a fuskokinsu. "Rigimace kawai" Murmushi yayi yace "Kuntota, kije ki kirawo Shafa muci abinci yau a mugun gajiye nake sosai" Umarninshi tabi ta kunto ƴar ta bashi, taje ta kirawo Shafa suka tawo tare. "Sannu da dawowa" Sai ya washe bakinshi yace. "Yauwa Shafa ya gidan, ina Abba?" Hadiza tana zuba abinci tana kallon yadda Gwadabe yake mata fara'a tana jin ciwo. "Bacci yake yi, yana kan kujera a falo" Tana faɗar haka zuruf ya miƙe ya ajjiye ummu akan kujera ya fice. Hadiza ta kalli ummi data canyara kuka, ta dubi Shafa taji wani abu ya riƙe mata maƙonlatonta. Sai ga gwadabe da Abba a kafaɗarshi. Hadiza ta ɗauki ƴarta ta goya ranta ya bala'in ɓaci sai taji abincin ya fitar mata ma aka. Allah ya taimaketa tana goya yarinyar sai tayi bacci. Suna tsaka da cin abinci sai Shafa ta fita a guje amai yazo mata. Da sauri gwadawa ya bita da Abba a hannunshi. Hawaye suka zubo ma Hadiza a kumatunta ta yi maza ta share hawayen ta rurrufe kwanukan abincin ta wanke hannunta ta shigewarta ɗaki tayi kwanciyar rub da ciki ummi na bayanta. Tuƙuƙin kishi zai murɗa mata yake yi. Gwadabe yafi awa guda kafin ya shigo. "Hadiza daure ki ɗan dafa ma Shafa tea sai ki haɗa da balango a cikin ledar dana shigo da'ita in kai mata" Namiji tuwon ƙaya miyar allura Tean ta haɗa ta kawo mishi da naman ita bata rabo da ruwan zafi a filas, nanma saida yafi minti talatin kafin ya dawo. Ya tarar Hadiza ta kunce ummi ta mata shinfiɗa itama tana kwance tayi shiru tana zubar da hawaye. Kwanciya Gwadabe yayi a kusa da'ita ya jawota jikinshi ya haɗa bakinsu waje guda. Daga nan labarin ya canja salo. Tsakanin mata da miji sai Allah. A daren Gwadabe ya wanke laifukanshi. Sukai baccinsu mai daɗi, da asuba ma bayan ya dawo masallaci ya jawota jikinshi suka koma ruwa. Shikenan fa maganar ta ƙare. Hadiza sai ta dena ƙorafi sam, duk abinda ta gani saidai ta cinye damuwar abun na cin ƙasan ruhinta. Laulayin dai ciki ya tabbata bil haƙƙi akan Shafa cikinne dai da'ita. Cikin irin mai shegen laulayinnanne Anty Badi'a sun dawo daga tafiya suka tarar da Shafa babu yadda take. Ko me taci amai take yi farfesun kifi ne kaɗai take ci ya zauna mata. Tama dena girki kwata_kwata farfesun kifinma indai ita tayi bata iya ci, sai Hadiza ta ɗauke mata. Shi kuma goga gwadabe fa ganin canjin da aka samu a wajen Hadiza sai ya zamana ya ƙara sonta, ya ƙara zagewa wajen kulawa da'ita. Kuma ya mata godiya sosai akan canjawar da tayi dan yaji daɗi gaya. Ita kuma matar Mammada Allah bai bata haihuwarba ita kaɗaice a cikin matan gidan bata haihu ba, duk matan gidan goyo suke yi, sai ita kaɗai da ko ɓatan wata bata taɓa yi ba. Ga Shafa ta samu ciki tana jin yayi wuri dama bata samu ba. Ga matar Mammada tana dama itace Shafa. Haka Allah dama yake yin ikonshi. A cikin gidan malam ta ɓangaren matanshi yawan faɗa da yawan rikici yayi sanyi sosai. Sai dai fa ko wacce ta ciki na ciki. Sunyi haƙurine sabida yanayin jikin Malam, da kuma sakin Baba Suwaiba da yayi. Wannan yasa Baba Asshi ta sassauta faɗanta dama itake haddasa yawanci fitintinun gidan. Tayi zuchiyar dena zuwa turakar Malam ma a tunaninta zaita binta yana rawar ƙafa akanta. Irin yadda yaima Baba Fhatsima data dena zuwa turaka, sai taga saɓanin haka. Ba shiri ta watsar ta koma akaci gaba da rabon kwana da'ita. Matar Malam kuma ciki gareta tana fama da laulayi, yau an bata gado a asibiti, gobe tana gida, yau amai, gobe yawu dai. Yaran matan da akaima aure, Malam ya kafa musu dokar dena zuwa mishi gida barkatai, sai matsalolin cikin gidan ya ragu. Sai matsalolin can gidan wanda wannan Yaya Tasi'u da Yaya Jamilu ne akai. Malam yama dena sanin meke faruwa. Ta ɓangaren Baba Fhatsima kuma ta roƙi Yaya Tasi'u ne akan ya auri Balaraba tunda ta lura har gobe suna son junansu. Ta bashi kwana biyu yayi tunani. Ya dawo bayan kwana biyun yace mata ya amince. To a halin yanzu hidimar haɗa kayan akwati akeyi. Harma an fitar da lifaran (ankon biki) Anty Badi'a ko da Yaya Tasi'u ya tareta da maganar ƙarin auren. Sai tayi mishi fatan alkhairi tare da yi musu adda'ar zaman lafiya. Jin daɗin hakanne yasa ya biya mata Umara. Ta tafi da kwana ɗaya aka ɗaura auren. Bikin daya tara ƴan uwa da abokan arziki. Amarya Balaraba ta tare a ɗakinta, akaita amarci. Saida suka cinye amarcinsu kafin Anti Badi'a ta dawo. Kafin ta dawo tazo ta tarar Yaya Tasi'u ya sake mata komai na ɗakinta, tayi mishi godiya, ta kuma rungumi Balaraba suke zaune lafiya, sai ɗan abinda ba'a rasawa. Wannan dalilin ya ƙara ɗaga daraja, girma, da kimar Anti Badi'a a wajen iyayen Yaya Tasi'u dama ƙannenshi ƴan ɗakinsu. Ta bangaren matan Gwadabe kuma rayuwar tana ta buɗe musu, Gwadabe yana ta samun ciniki. Kwatsam ranar wata Juma'a sai ga kiran Zulƙi yana sanar da Gwadabe akwai taron manya da za'ayi a garin Abuja ranar monday. Yana so gobe yaje Takai ya sameshi sai su wuce taron tare ya tafi da maganinshi. Ai kuwa hakan akayi shadda kala biyu Gwadabe ya ɗinka, ya sai takalmi mai tsada da hula. Ya ɗauki akwatin magungunan shi yaima matanshi sallama sai Takai. Kwananshi ɗaya a wajen Bara'u ranar Lahadi suka shiga Abuja. Washe gari Gwadabe yabi Zulƙi zuwa wajen taron. Kamar wata ƴar liyaface aka haɗa na Gwamnoni, da ƴan majalisu, da Chiyamomi, harda sarakuna. Alkhairi da Gwadabe ya samu a wajen wannan taron bana wasa bane. Saida ya saida maganinshi tas ya dafe kuɗaɗenshi. Suka sake kwana a Abuja. Washe gari Gwadabe ya dawo Nijar, Zulƙi ya wuce Takai. Cikin dare Gwadabe ya shiga gida, a ɗakin Hadiza yake harta yi bacci sai gashi. Yayo musu tsarabar sutura, da kayan kwalliya da turare. Kuma yai musu ihisani da kuɗi mai ɗan tsoka. Sukaita shi mishi albarka. Shafa kuma ya bata kuɗin siyan kayan jariri ta soma ajjiyewa duk da cikin watanshi ukune kawai, ganin ya samu kuɗine yake ganin bari a soma ragewar dai, tunda shi ɗinne dai zai siya. MRS BUKHARI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU 12 IYABO "Wai Iyabo laulayi kike yi ne, ko ciwo kika yi mun yi waya har sau biyu dake baki sanar mun ba? Anya kina kallon mudubi kuwa? Kin ƙare kin lalace ko dai babu zaman lafiya tsakaninki da Hamma ne. Ga ɗakin kishiyarki na leƙa sai naga wayam. Ajjiyar zuchiya na sauke nace. Uwani halin da nake ciki yafi ƙarfin duk wannan lissafin naki. A cikin dabaibayi nake, cikin rijiya mai gaɓa dubu." Wasu siraran hawayene suka gangaromun nayi sauri na share su. Labari naba Uwani na halin da nake ciki. Saida ta zubar mun da hawaye bayan ta gama saurarena. "Yanzu kina cikin irin wannan halin mawuyaci kika kasa sanar dani Iyabo? Kuma sai yanzu kuka yinƙura neman magani ma?" Uwani ina kai kukana wajen Allah shine zai mun maganin duk abinda ke damuna. Ni ko gidan magani da Yaya Hamman yace muje yau bana son yi mishi musu ne kawai shi yasa zanje. Amman da shawartata yayi da kukana zanci gaba da miƙawa wajen Allah yana sane dani bai mance dani ba. Ni garinne ya fitarmun akaina, auren ma ya fice a raina, sai inji kamar in yi ficewata in tafi ma kawai." Uwani ta dafani tace. "Komai yai tsanani sauƙi na nan zuwa. Duk abinda yai farko dole yai ƙarshe Iyabo. Amman kam kishiyarki ce tayi miki asiri ko kin ƙi, ko kinso tunda ai ta faɗa miki sai zaman gidan ya gagareki, kuma sai kin fita tsirara. Rashin bacci ai somi_ somin haukane. Amman muje wajen mai maganin muji me zaice mai kuma zai bamu. Kinga tashi kawai muje gidan matar abokin Hamman kawai mu wuce." Ko abinci Uwani bata ci ba, ta dai sha ruwa. Allah yasa abincin dana dafa tazarce nayi har dare na cika babbar kula na dare. Sallama naima Yafendo nayi mata ƙaryar zamu je gidan Cubu Uwani ta gano ɗakin. Muna fita sai gidansu Baɗejo, dama matarshi a shirye take goyo kawai tayi muka wuce wani ƙauye gaba damu sosai, munyi tafiya a mashin mai nisa kafin muka iso. Malamine sak ba boka ba, dama Yaya Hamma yayi mun bayani. Sai naga zahiri harda almajirai gasu a gabanshi. Amman layi ma ake bi ga mata da maza anata layi. Mun daɗe sosai kafin ma layin yazo kanmu. Ni kaɗai na isa wajen nai masa bayanin dalilin zuwan nawa tsab, da duk yadda nake ji, harda furucin da Hama tayi a kaina. Kai ya girgiza da lalatacciyar hausarshi yace. "A lalle haukatakin taso tayi, tunda ko runtsawa bakya yi, ƙarfin adda'ar da kike yi ne yasa burinta bai cika ba a kanki ba. Amman Allah ya fita. Yarinya ni ba boka bane, bana ba da laya. Sai dai zan rubuta miki ayoyin Alkur'ani in rubuta a allo in wanke miki. Sannan zan miki tofi da zaki dinga shafe jikinki, da habbatus sauda da zaki dinga turare ɗakin ki dashi. Ba asiri ba ko sammu akayi miki da izinin Allah saiya karye. Amman sai zuwa gobe zaki dawo, sannan ki dena kwanciya da janaba, ki dinga alwala kafin ki kwanta. Allah ya ƙara sauƙi gobe uwar haka sai ki dawo" To Malam Nagode sosai. Nawa zan bayar abun sadaka?" Murmushi yayi yace Sadaka bata kaɗan bata yawa, abinda Allah ya hore miki ajjiye ki tafi, inma baki dashi zanyi miki dolena." Nera dubu guda na ajjiye ina godiya na samu su Uwani muka kama hanya. Sai la'asar sakaliya muka shigo, a lokacin matan gidan duk sun daddawo anata aikace_aikace. A ɗakin Baɗɗo duk muka zube, muka yi Sallah. Baɗɗo suka gaggaisa da Uwani ta fita ta bamu waje "Iyabo wani tunanine ya faɗo mun. Kin tuno da wannan adda'ar ta karya sihiri wadda na baki akayi yima Gwadabe mai ganyen magarya? To yau ba sai gobe ba kiyi" Idanuna na lumshe tare da yin hamdala ga Allah. Na mance da wannan maganin karya sihirin in banda yanzu da Uwani ta faɗamun. Ai babu wata wata na aiki Baɗɗo ta ɗebo mun ganyen magarya a ɗakina guda bakwai, ta kawo mun ruwa a bokiti na tottofa duk ayoyin ban mance komai ba. Na adana bokitin anan ɗakin. Uwani wallahi na sha'afa da wannan magani na karya sihiri, daga yanzu in Allah yaso ya yarda bazan sake rabuwa dashi ba, lokaci zuwa lokaci zan dinga wanka da sha, tunda jarabawar gidannan ta kishiya mai asirice." "Wannan shi ake kira nama ya dahi romo ɗanye. Uwar miji a gidan auren fari ta hanaki saƙat. Wannan gidan kuma kishiya na neman rayuwarki. Ga kaya duk na siyo miki komai tashin hankali ya hanamu maganar kayan ma" Dariya nayi mata nace. Ke dai bari ana takai wa yake ta kaya? Bari inje in samu in watsa ruwa me gidan yana hanya. Ga kiraye_kirayen sallar magriba anayi." A ɗakin Yafendo nayi Sallah, kana na fito na raba abinci, ina kan rabawa Yusufu yazo karɓa musu na zuba musu nasu da nasu Dada. "Adda ance in faɗa muku Cubu bata da lafiya tana kwance a gida" Da sauri na ɗago na kalleshi. Meke damunta Yusufu?" Yace. "Ban sani ba dai, amman ance ciwon sosai ne" kwanukan abincin na miƙa mishi. Allah ya bata lafiya, gobe zanje in dubata. Ku kara haƙuri kunji ko Yusufu? Kaine babban kanka a yanzu kayi ƙoƙarin kulawa da kan ka. Duk abinda kuke buƙata kazo ka sanar mun kaji ko?" "To Adda, bari in tafi sai da safe" Yai mun sallama ya tafi. Ina fitowa Yaya Hamma na shigowa. Da sauri na ƙarasa na karɓi ledar hannunshi nayi mishi barka da dawowa. Daga ɗakin Yafendo kai tsaye masallaci ya wuce. Duk muna tsakar gida kowa na sha'anin gabanshi. Sai da naga wucewar Yaya Hamma ya nufi ɗakina na bishi ɗauke da tiren abinci. Saida na jima ina addu'a kafin nasa kai na shiga ɗakin. Wannan tashin tsigar jikin dai saida naji, kuma sai inji anyi tsaye a kaina. Shiru nazo na samu yaya Hamma ba dai yadda na saba ganinshi ba, kamar akwai damuwa a fuskarshi. Yaya Hamma lafiya kuwa na ganka a cikin damuwa?" Ajjiyar zuchiya ya sauke ya dubeni yana dariyar yaƙe. "Babu komai halin rayuwane, yau da gobe kinsan sai Allah. Ya jikin naki, kunje wajen maganin?" Ajjiyar zuchiya na sauke kana nace. Munje harda Uwani ma, da rana sai gata tazo" Ya yi dariya yace. "Uwani ƙawar amana kenan. Allah sarki. To yaya kuka yi da mai maganin?" Na labarta mishi yadda muka yi, yana saurare yana cin abincinshi. Abincin loma biyu yayo ya ajjiye. Furarma kurɓa biyu yayi kawai ya rufeta. Ni gabaki ɗaya na kasa gane mishi. Na tambayeshi yace babu komai. Bana son in matsa mishi dole in barshi, sai dai in naga damuwar tafi haka yawa dole in kuma tambayarshi. "Zanje wajen Baɗejo ba daɗewa zanyi ba. Kema nasan ɗalibanki suna tsakar gida suna jiranki." Tare muka fito, shi yayi waje ni kuma na ƙarasa wajen ɗalibaina mu kai karatun dai babu armashi yanayin yadda naga Yaya Hamma zahiri a cikin damuwa yake. Bamu kai lokacin tashi ba na sallamesu, na faɗa musu na kawo kayayyakin mata gobe kowacce ta kullo kudinta zan buɗe haja. Suna cikin murna Yaya Hamma yazo ya wuce mu. Da idanu na bishi jikinshi duk a sanyaye ba laka. Jikina a mace nabi bayanshi a kwance naje na sameshi yana kallon sama. Ƙur na ƙura mushi idanu ina nazarinshi. Yaya Hamma dan Allah menene matsalarka ya kamata ka sanar dani damuwarka karka sani a wata sabuwar damuwar" Tunda nake magana yake kallona, hannayenshi ya miƙo mun halamun inje. Banyi musuba nabi umarninshi. "Babu komai Jabu. Ki dena damun kanki bana jin daɗin jikin nawane yau shiyasa tun ɗazu a wajen aiki nake jina wani iri. Magani naje Baɗejo ya bani nasha." Nan na shiga aikin yi mishi sannu. Wannan dare ya bamu wuya sosai dan har ji nayi kamar ana kiran sunana. Sassafe na yi amfani da wannan tofi, na sha na shafe jikina dashi tas. Abun da yafi komai bani mamaki a madadin Yaya Hamma ya tafi wajen aiki sai kawai na ganshi ya koro shanu ina duƙe ina wanke kayan yaranshi da nashi. Tsayawa yayi suka gaisa faram_faram da Uwani ya dubeni da sandarshi a wuya yace. "Ni zan tafi kiwo ki mun addu'a Murmushi nayi nace. Ubangiji Allah ya kareka da kai da shanun a shiga jeji lafiya a fito lafiya" Kallona naga yanata yi, ni dai saina tsinci gabana da faɗuwa. Harya fice a gidan na wanke hannuna na bishi. Uwani ina zuwa" Ina fita na sameshi a ƙofar gida yayi shiru yana kallon shanun, suma duk sun tsaya suna jiran shugabansu ya kirasu su soma tafiya. Yaya Hamma yau baka da aikine zaka tafi kiwo?" Ɗagowa yayi ya kalleni. A madadin ya bani amsar tambayata sai yace dani. "Ina sonki ina ƙaunarki duk runtsi. Wannan halin lalurar da kike ciki yana tayar mun da hankali tunda a gidana kika samu wannan lalura, ga rasa idanunki da kika yi sanadiyyar dukan da ni Hamma nayi miki kaicona, ina tsoron ranar da zaki gaji da wannan auren ki nemi barin rayuwata Jabu, ina tsoro da fargabar wannan rana. Akwai wani mai magani da aka kwatanta mun in an gwada na malamin da kika je wajenshi baiyi ba, zan ɗaukeki in Kai ki can wajen wancan. Kiyi haƙuri Jabu, kinsan dai ina sonki kuma lalurar ta dameni ko?" Ga murmushi a fuskata ga hawaye inayi. Ina bala'in son Yaya Hamma ku kunsan komai, kuma duk sanadiyyar aurenshi ne nake samun wannan matsalolin, inajin auren ya fice a raina, inajin ƙauyen ma ya isheni ƙarfin sonshi da nake yi ke riƙe dani a ƙauyen da ƙarfin adda'a. Amman a kullum sai in dinga ji kamar in zunduma ihu ko in fice a guje. Da zaran naji hakan ya bijiromun sai inta karanta la'ilaha'illah anta subhanaka inni kuntu minal zalumin, hasbunallahu wa'ni'imal wakil, la haula wala ƙuuwata illabillah. Sai inji dama dama. Duk rintsi ina tare dakai Yaya Hamma. Bana fatan zuwan ranar da zan gujeka kasa a ranka zamu kasance har izuwa ƙarshen rayuwarmu. Soyayya ba ƙarya bace ina maka son so domin Allah ka yarda dani ka dena fargabar zuwan ranar da zan gaji da aurenka. Babu wannan ranar, bakasan girman matsayinka a zuchiyata bane." Murmushi yayi mun, nima na mayar mishi da murmushin ina share hawayena. "Nagode Jabu yanzu kin ƙaramun kuzari, nutsuwata ta dawo jikina ni zan tafi kiwo" To Allah ya tsare mun kai ya kareka. Inaso inna gama aikace_aikace zani gidan Cubu ance bata jin daɗin jikinta" "Assha to Shikenan sai kin dawo, kya gaisheta" Da haka mu kai sallama na koma cikin gidan. Ƴan tsurko sai kallona suke yi, ni ko bansan ma suna yi ba. Nazo na tarar Uwani ta gama wankin ɗauraya take yi. Tare mu kai shanya muka je ɗakin Yafendo muka karya. "Jabu kwanannan ina lure dake bakya komawa ɗaki har sai wannan yaron ya dawo ko ƙarfe nawa zai kai. Ga rama kinata yi, inna tambayeki Jabu sai kice babu komai. Amman ni ko a fuskarki inna kalla sai inga damuwa ƙarara. Ki sanar dani abinda ke damunki Jabu, ni Mamanku ce baki da wacce zaki sanar ma matsalarki daya wuce ni, ko dai rasa idanunki guda da kika yi ne kika saka abun a zuchiyarki yake ta nuƙurƙusarki? Ki sani bawa baya wuce ƙaddarar da Allah ya ƙadarto mishi. Kuma har gobe bamu cire rai ba anata neman magani in da rabo sai kiga idon ya dawo kinci gaba da gani dashi. Murmushi nayi kamar yadda na saba, kaina na ƙasa gudun karta gane ƙarya nayi mata nace. Babu komai Yafendo. Wannan ramar ta canjin yanayi ne kawai, sai ɗan zazzaɓi dake damuna a tsaitsaye kuma ina shan magani. Rashin shiga ɗaki zafine kawai yayi yawa dake a cikin zafin muke. Sai naga tana murna ƙila tana tunanin ko ciki ne dani. Au ai kuwa makon jiya ya kamata inyi jinin al'ada kuwa amman banyi ba. Na faɗa a raina" "To masha Allah. Muga hannunki " Saina miƙa mata, ta duba tafin hannuna sai tayi dariya tace. "Sai ki dinga yin komai a hankali. Girkinma ki dena yi Baɗɗo in tayi ta zuba miki, ke dai kiji da kanki, wannan yaron abinci ba damunshi yayi ba dama" Duk sai kunya ta lulluɓe na fahimci dai Yafendo taga ciki ne dani. Sai naji wani farin ciki marar musaltuwa nake jina kamar wannan cikin shine cikin fari. Allah ya bani mai albarka, wanda zasu ji tausayina. A nan Yafendo ta fita ta barmu anyi haihuwa a maƙota zata shigar musu barka. Na sanar mata zamu shiga muma gidan barkan, daga nan kuma zamu je gidan matar Baɗejo. "Ke baki san ma kina da ciki ba? Ni ko kinga ina ganinki ki kai mun kama da masu sabon ciki sabida naga kinyi haske. Amman da banji kince kina da cikin ba sai nake ganin ƙila sabida ramar da kika yine yasa kika yi fari. Nifa na mance ban faɗa miki ba Gwadabe yaje gidan Hajiyarmu nema na fa" Take gabana ya tattake ya faɗi, zuchiyata ta tsinke jin an ambaci Gwadabe. Na yi jim ina tuno Gwadabe na, da irin rayuwar da muka gudanar duniya kenan. A duniya banyi tunanin ko a mafarki aurena da Gwadabe zai ƙare ba. Bayan ya ƙaren banyi zato ko tsammanin zan so wani ɗa namiji rabin yadda nake son Gwadabe ba. Ashe ba haka bane so da ƙaunar Yaya Hamma a zuchiyata ya dakushe tauraruwar Gwadabe a zuchiyata ta yanda ba'a iya hango ƙyallinta ko misƙala zarratan. Sai dai ina gani girma Gwadabe fiye da kowa, ina girmama ƙoƙarinshi a kaina. Yarana suka faɗo mun ai sai hawaye." "Au harda kuka Iyabo dan kawai na ambaci sunan tsohon mijinki?" Gwadabe yafi ƙarfin kawai Uwani kema kin sani. Kar kiyi tunanin da ɓirɓishin son Gwadabe a zuchiyata alhalin da aure a kaina. Wallahi ko ɗaya, kuma nasan yin hakan laifine. Sunanshi da kika ambatane ya tuno mun da irin zaman da muka yi. Kukan da nayi kuma yarana na tuno kawai. Neman me Gwadabe yake miki, neman jin labarin inda nake ko? Gwadabe manya. Ina mishi adda'ar Allah yasa yana cikin aminci tare da yarana, ina mishi fatan samun macen da zata soshi fiye dani " "Kamar kuwa kin sani. Har lambata yaso karɓa Hajiya ta hana tana gudun kar Hafizu ya zargi wani abun. Kinsan tunda na soma kasuwanci Hafizu ya soma mun baƙin ciki, da yaga maza sai ya koresu a shagona. Na kulle gidan na koma gida satina daya yaita sintiri kinsan ba zuchiya gareshi ba, ga talauci na damunshi a gidan nawane yake samun abinci me kyau ya kwanta a lallausan zanin gado. Nifa Allah auren Hafizu ya fita raina. Kuma a yanzu haka ciki gareni, amman inaga ko wata ɗaya baiyi ba ma To Hajiya dai ta faɗa mishi kina aure a garin da mahaifiyarki take. To sai dai tace ta mance bata tambayeshi yayi aure ko baiyi ba. Ta dai tambayi yaran yace suna cikin aminci sunata karatu" Allah sarki Gwadabe nagode sosai. Inason ganin ƴaƴana in sha Allah inna shigo Kano zan ɗaukeki mu shiga takai ko tsirenine Babala sai dai tayi" "A'a ki rufa ma kanki asiri. Mijinki kishinshi da yawa kiyi zamanki ni zanje in dubo miki su da izinin Allah. In kuma sun girma babu mamaki Gwadabe ya dinga kawo miki su su kwana biyu. Amman ki samu matsalolin da kike ciki su warware. Wato Iyabo idon naki ya mutu da guda ɗaya kike gani? Allah mai iko mata muna ganin jarabawa iri da kala a gidajen aure, sai dai muce Allah ya bamu mafita. Tashi mu je mu dubo Cubu, daga nan muje gidan Dada ko?" Sai da mu kai wanka, Uwani ta shiga ɗaki ta ɗakko mun kaya nasa. Mu ka je ɗakin Baɗɗo ta tayani muka buɗe dila sabida ta cika ma Baɗɗo ɗaki, inaso in raga mu kai gidan Dada. Kayane gangariya na yara, mis dana jarirai masu kyau. Na jariran muka ware waje guda basu da yawa sai kawai nace ni da uwani mu raba tunda cikine damu. "Aa ni na tara kayan jira jirai da yawa kin mance na saida dilar kayan yara? Ki ajjiye dai zasu miki amfani, tunda basu da yawa sai kawai ki ɓoyesu kinga in aka baki kuɗin kya yi wani abun dasu." Muka ware kayan kashi kashi. Muka ɗaubi ƙunshi biyu wanda zamu tafi dashi gidan Dada na ware ma yaran Hamma, da yaran Baɗɗo, da yaran Amaduyal, Safiya ma na ɗaukarma yaronta guda ɗaya, matar Baɗejo ma haka. Me jego da zamu shiga mata barka ma zanzo in duba mata kala ɗaya ranar suna in bata dan muna mutunci sosai ta kanyo zuwa na musamman wajena mu yi hira duk ranar da bata je tallar Nono ba. Da muka fita gidan Dada muka soma zuwa sabida kaya da muka doro a ka ni da Uwani niƙi_niƙi muma muka saje da matan ruga. Daga gidan Dada ne bayan mun yi azahar sai muka tafi, na ba Dada ɗari biyar nace ta yi musu girki ga yaran Jatau ma suna gidan suna wasa. Da Sallama muka shiga gidan Cubu. Kishiyoyinta suna tsakar gida ko wacce na aikin gabanta. Gidan a share yake ƙal suna da tsafta sosai ko bokatan gidansu babu kazanta a jikinsu labulayen bukkokinsu kuwa tas'tas haka jikkunansu ma tas. "Sannunku Jabu anzo duba marar lafiya kenan?" Cewar kishiyar Cubu wacce acewarsu ita akaima kishiya tunda kafin zuwan Cubu itace Amarya, mata ta uku kenan. Na fahimci kamar tafi sauran guzumayen sauƙi dansu sunci sun ƙoshi suna da manyan yara gaisuwar arziki basa amsawa ni shi yasa ko kallonsu banyi ba. Na amsa ma kishiyar Cubu da cewar. Wallahi kuwa nace dai bari inzo in dubata. Ina wuninku?" In kun tanka sun tanka mu dai muka shige bukkar Cubu tana kwance ba yadda take duk ta bushe ta komaɗe, ga zafi amman tana ƙunshe a ɗaki tana fifita. Ganinmu ne ma yasa taji daɗi. Cubu kina zaune ke kaɗai a wannan zafin ga matan gida a waje kowa na shan iska ba zaki fita rumfarki ki sha iska ba?" Cikin rawar murya tace. "Adda inna fita sai suita zubar da habaici suna zagina wai Dadana ma taƙi zaman aure da girmanta amman aurenta ya mutu, mu bamu da tarbiyya muna ma kishiyoyin Dada rashin kunya. Dake kishiyata ta biyun ƙawar Baba Dije ce, ko ɗazu Baba Dije tazo wajenta. To Adda sai suita azabtar dani, kuma ranar girkina babu wanda yake taimakamun, ko da bani da lafiyannan basu ɗauke mun komai ba, kuma ina jin ƙaurin kara zanta hararwa" Ƙuri muka zuba mata ido ni da Uwani. Kafin muyi magana sai ga kishiyarta da nono cikin ƙwarya yaji sikari da dambu ta ajjiye mana. Cubu har wannan kishiyar taki da naga kamar tafi manyan kirki bata taimaka miki?" Sai Cubu ta ɗanyi murmushin da yafi kuka ciwo. "Adda wannan matar muguwar makirace tunda nazo gidannan take ƙullamun makirci a wajen mai gidan. Bata so taga ya ambaci ko sunana" Uwani tace. "Amman yaya tsakaninki dashi kuna zaune lafiya baya cutar dake?" Cikin kunya tace. "Baya cutata, yana bani haƙuri kullum akan halayen matanshi shima sunfi ƙarfinshi ne. Kuma yana kawo mun nama da lemun kwalba a ɓoye, shi kaɗai nake iya ci" Ajjiyar zuchiya muka sauke dukkanmu. Uwani tace. "Komai zai zo miki da sauƙi tunda mai gidan baki da matsala dashi. Shawarata anan shine ki zage ki ƙwaci ƴancinki babu wanda zaizo ya ƙwatar miki ƴanci. Karki bari habaicinsu ya hanaki fita ki wataya, yadda kowa yake a zube a tsakar gida yana shan iska kema ki dinga fita. Yanzu lallaɓa ki fita mu gyaggyara miki ɗakin naga duk tarkace, in kin samu lafiya ki roƙi mijinki ya saki a makarantar dare da Iyabo take koyarwa kema ki samu ilimi." A darare Cubu ta fita, kai kawai na girgiza ina mamakin wannan rayuwa. Tas muka gyare mata ɗakin nata kayan wankinta Uwani ta haɗa tace zata tafi dashi ta wanko Yusufu ya kawo mata. A tsakar gidan muka sameta tanata sheƙa amai uwargidan tana kanta tana faɗa akan tana musu ƙazanta kamar a kanta aka soma ciki bayan ta shigo gidan ta gansu da ƴaƴansu. Ta inda matarnan take shiga ba tanan take fita ba. Mu dai bamu ce komai ba Uwani ta gyara wajen ta zuba ma Cubu ruwa ta wanke mata fuska ta kamota suka dawo tabarma ta saka mata fulo ta kwantar da'ita." Sannu Cubu. Zan yima Dada magana a turo miki ko Hassanan Hari ta ɗan dinga taimaka miki, tunda Jatau ya ba Dada ita ba'a barki ke kaɗai ba. Baɗɗo zata dinga zuwa dubaki akai_akai Allah ya ƙara sauƙi " Mu kai ficewarmu ba tare dana amsa a sauka lafiyan da Kishiyar Cubu take mana ba. Muna tafe da Uwani munata tattauna matsalolin da mata suke fuskanta a gidan aure, sai dai muce Allah ya kawo mana ɗauki. Da Sallama muka shiga gidan mai jego matan gidan ba kowa ko wacce ta tafi tallar Nono, sai wata tsohowa da inaga mai kula da mai jegonce. "Maraba, ku shiga tana ciki me jegon" Uwani ta ajjiye ƙunshin kayan hannunta muka shiga muka samu mai jego a zaune tana ba jaririyarta Nono. "Ah malama sannu da zuwa. Kinga kuwa yanzunnan Hama ta shigo taimun barka ta fita" Zama mu ka yi a tabarma ta miƙo mana jaririyar. Jikina a mugun mace nace. Allah sarki ta shigo kenan sannu mai jego" "E yau ta dawo maƙota ma nata zuwa mata barka, ƴan tsurku ma suna yi maganganu sai yawo suke. Baiwar Allah ina wuni?" Ta dubi Uwani da fara'a ta gaisheta. Ita kanta uwani jikinta a mace ta amsa. "Lafiya lau ya jiki Allah ya raya abinda aka samu" Ni dai gurum nayi ina mamaki Yaya Hamma yasan matarshi zata dawo shine bai sanar dani ba. Hmm maza ho halinsu sai su. Jaririyar na miƙa ma Uwani ina tambayar me jegon Gobe ne sunan ko?" "E gobe ne Malama. Naji anata labarin magungunan da kika kawo da kayan kwalliya nima dan Allah inaso malama tunda nima ɗalibarki ce." Murmushin dole nayi nace. To babu damuwa, gobe zan shigo da safe taya aikin abincin suna zan tawo miki dashi. Akwai ɗan kunne da sarƙa fella_fella in kina so" MRS BUKHARI B4B ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (13) IYABO "Inaso Malama a tawo mun dasu in zaɓa. Kuma inason jar hoda in akwai" Ta ƙarashe zancan tana Dariya. Nima dariyar nayi mata na miƙe. To Allah ya raya zan tawo miki dashi Uwani tawo muje ko?" Muna fitowa sai ga matar Baɗejo ta shigo barka. "Ah Malama ashe kina nan, yanzu nake cewa in nayi barkar zan shigo miki mu samu muje mu dawo da wuri." Kinganni nazo barka, muma dama daga nan gidanki zamu je, shiga kiyi barkan muna ƙofar gida" Shiga tayi mu kuma mu kaima wannan tsohuwa sallama muka fito. Uwani ina cikin matsala. Matsalata ta dawo" Uwani tace. "Hamma ya faɗa miki dama zata dawo ne?" Kai na girgiza mata halamar a.a ta kwashe da dariya tace. "Maza mutananmu ɗan munafurcinnan ba'a rabasu dashi. Ni damuwata ɗaya wannan halin da kike ciki ke kaɗai zaki dinga kwana kenan? Bari inje in ajjiye wannan kayan wankin in fito tukunna." Ni dai har Uwani taje ta dawo ina tsaye kamar gunki ina tunanin yadda za'ayi in kwana ni kaɗai a wannan ɗakin. Bazanma taɓa iyawa bane wallahi sai dai Hamma yasan yadda zai yi dani ko mu haɗu mu kwana tare a ɗaki ɗaya ba. "Iyabo harna dawo baki ma san na dawo ba. Almurar da danginta sunata shigar mata da kaya. Harda sababbin kujeru na gani a tsakar gidan irin marasa hannunnan. Sai wani bina suke da ido, inajin shegiyar tana musu yare nasan dai gulma ce." Fitowar matar Baɗejo ne ya hanani tankawa muka rankaya inda zamu hau abun hawa. "Ashe Hama har ta dawo? Jiya inajin Baɗejo suna zancan dawowar tata da daddare da Hamma ya shigo. Akan maganar motar da zata je ɗebo kayanta" Namiji tuwon ƙaya miyar allura, duk yadda kake da namiji in yaso yin munafurcinshi sai yayi, shi da yace magani yaje ya sha a wajan Baɗejo ashe ƙaryace. Murmushi nayi nace. E haka yake sanar dani batun dawowar tata nima." Babu daɗi babu ragi naja bakina nayi shiru. Ina kan acaɓa ina mamakin maza har muka isa wannan ƙauye. Yau bamu tarar da layi sosai ba, malamin ya bani rubutu a gora, ya bani tofi shima a gora sai hayaƙin habbatussauda da yace dana ga dare yayi in banke ɗakina dashi, bayan na gama komai sai in yi alwala in sha wannan rubutu, shi kuma tofin in tsiyaya in shafe jikina dashi in sha Allah matsalata ta kau. Godiya nayi mishi sosai muka sake kamo hanya kafin mu iso magriba har ta kawo kai. Ina saka ƙafata a ƙofar gidan ɗago ɗayar da zanyi in ajjiye a inda zan ajjiyen sai naga wani farin ƙyalle. Allah ya taimakeni ban taka ba sai nayi tsalle na shiga gidan. Uwani ta kewaye ƙyallen ta wuce. Allah al hakim wai wannan bala'in duk akan ɗa namiji akeyinshi wai shin me na tare ma Hama ne da take haɗa mun masifa da bala'i haka?" Uwani ce tai bismillah ta ɗauki ƙyallen muka shige. Ina jiyo surutun mata a kitchen anata shewa. Baɗɗo kuma fitowarta daga bukkarta kenan. "Adda sannunku da dawowa. Ai kuwa yanzu wannan matar mai sarin kaya tazo nace mata bakya nan. Amman tace gobe da wuri ma zata zo dan nace mata kin kawo kaya." Wallahi in yi magana na kasa sakamakon haɗa idanu da nayi da Hama. Taci uwar kwalliya ta sha sabuwar atamparta dal. Tayi wani irin kyau har baƙin ƙunshi tasha hannu da ƙafa, ga kitso an yarfa mata zai iya fin guda ɗari ya zuba kawai a kafaɗarta. Wani kishine ya tsargamun da ganin kyan da Hama tayi. Wanda yake da Hama banga abinda zaiyi da Iyabo ba, ba dai kyau na fuska dana fata ba sai dai diri da tsoka kawai za'abi. Ta gabana tazo ta wuce tana kwarkwasa da sabon filas dinta a hannunta. Hama ashe har kin dawo tun ɗazu, da Yaya Hamma ya faɗamun nayi tunanin sai da yamma zaki dawo shi yasa ma ban ajjiye miki abinci ba, sannu da dawowa " Da sauri ta juyo ta kalleni, nifa da ƙyar na danne kishina harna saurareta sai cemun tayi. "Kinsan da dawowar kenan ya faɗa miki ke?" Ai sai naji wani farin ciki dana lura kura zan kunto mishi. Kwarai na sani sosai ma. Ai dani akaita komai har zuwa wajenki da yake yi nice nace ya dinga zuwa, ya kuma dinga miki kyauta" Ina faɗar haka na yi shigewata ɗakin Baɗɗo na ajjiye kayan magungunana, nayo alwala muka yi sallar la'asar, muna kan sallah akayi kiran magriba. Na idar ina zaune a dadduma na yi tagumi Uwani fa sai magana take mun naƙi kulata. "Adda akwai ruwan wanka a madafi a murhu ko zaki kwatsa ruwa?" Zan watsa Baddo. Uwani wani tunanin na lula ina jinki ke dai bara in fito" A gurguje nayo wankan haɗe da alwala. Hama fa sai giggiwa take yi kamar sabuwar bera. Murmushi nayi a raina nace. Yau zaki sha mamakina wallahi Allah saina saki zubar da hawaye zan nuna miki bariki yau." Ɗakin Baɗɗo na shiga nayi sallata a nitse duk ƙuncin da nake ciki ya yaye, na jawo bokitin wannan tofi na soma amfani dashi sannan na shafa na wannan malamin. Uwani tawo muje ɗakina maci tuwon acan. Baɗɗo kiyi haƙuri in Yusufu yazo ki loda mishi wasu kayan ya kai gidan Dada na cika muku ɗaki da shirgi" Hannun uwani naja muka fito, Hama na kofar ɗaki ta kafa ta tsare za'a amshi miji muka zo muka wuce da gaushina cike da kasko, da bismillah na shiga na lalubi tocilata a saman kujera na kunna haske ya game ko'ina uwani ta samu ƙasa ta bararraje da tuwonta. Zauna kici tuwon yau za'aga jarfa a gidannan uwani ke dai zaki sha labari. Hayaƙi na zuba a gaushi na tafi sib ina nemo kaya ina addu'a tsigar jikina sai tashi suke kaina na buɗewa. Doguwar rigar gumama na saka mai baiyana shape gata da sulɓi ta sama ta kamani tayi caras a jikin nawa, ta ƙasa ya buɗe ta baya daidai mazaunaina rigar tayi ɗare_ɗare saman mazaunaina. Na fesa turaruka kala_kala harda wanda ma ban taɓa fesawaba na ɓaresu a kwali. Baɗɗo ce tayi sallama ta shigo da nono a hannunta ta dure a gaban Uwani. "Adda ɗalibai sun gama cika fa ke muke jira yau naga harda sababbin fuska ma". To Baɗɗo Yaya Hamma nake jira har yanzu naji shiru na jiyo ɗuriyar su Nasiru amman shi har yanzu shiru" Ɗan murmusawa tayi tace. "Ya dawo tun ɗazu fa Adda. Ya jima a cikin gidanma ai" Murmushi nayi mata na fice na barta nan. Karatun kanshi baifi na minti talatin akayiba hankalina na ɗakin su Hama da nake ta jiyo dariyarsu. Magunguna da kayan kwalliya dana fito musu dashi warwaso suka yi ma komai. Magani kam ya ƙare tas in banda wanda na cire ma kaina, da wanda na cire ma Baɗɗo, da me jego. Kayan kwalliyarne su kai ragowa nai musu bayanin da bai wuce minti ashirin ba na sallamesu. Ina zaune a turmi ni da uwani da Baɗɗo muna hirarmu, yaya Hamma ya fito suka gaggaisa da su Uwani yace "Jabu ina ɗaki ina jiranki" Ya nufi ɗakina nabi bayanshi da uwar muguwar harara, na miƙe. Sai da safenku Uwani ma ƙarashe gobe" Na shiga na sameshi a tsaye yama kasa zama ina kallonshi ai saina danna ihu na rungumeshi ƙam na rufe idanduna ruf, basai na hau ɓarɓarɓar da jikina ba halamar matsanancin tsoro ba. Gogan naku duk yabi ya rikice sai tambayata yake yi, wallahi naƙi bashi amsa saima wasu surutai da sokiburutsun zance dana shiga yi mishi kamar zautacciya. Zan mutu Shikenan zan mutu in barka, ga danƙa a cikina ashe babu rabon zaka ɗauki ɗanka wanda nice uwarshi ka yafe mun" Naita ɓarin zantuka ras fa nake nayi rantsuwar bai isa ya kwana a ɗakin Hama bane yau inaso in nuna mata shegen birni gaba yake da shegen ƙauye kuma shima duk bala'in kwaɗayinshi saidai ya haƙura. Da ƙyar Yaya Hamma ya iya jana zuwa bakin gado muka faɗa gadon tare na wani sandare kamar na mutu. Ai a guje ya danna a guje ya fita. Idona na buɗe nace. Kaɗan ai ka gani ma ba kai munafuki ba. Bai jima ba sai gashi ya dawo tare da Yafendo, da Hama, Baɗɗo da Uwani. Ruwa ya yayyafa mun nayi ajjiyar zuchiya mai ƙarfi, naƙi buɗe idanuna ma balle mu haɗa idanu sai kuka. "Allah ya bata lafiya. Yanzu abinda za'ayi kai ka kwana tare da'ita kaita mata adda'a inaga wannan abun harda junnu. Gobe sassafe zanje in karɓo mata magani. Ku mu jenku. Jabu Allah ya tashi kafaɗa. Allah yasa ba sabida juna biyun dake jikinta bane aljanu ke son shafarta ba" yaya Hamma inaji yana tambayar Yafendo dama juna biyu gareni shi bai sani ba? To kunsan kunya irinta fulani sai ma ta fice a madadin ta kulashi sai Uwani ce ta bashi amsa. "Juna biyu gareta ai Hamma. Dan Allah ka kula da'ita gashi gobe ni zan koma da sai in zauna da'ita. Duk da dai tafi bukatarka fiye damu. Baɗɗo muje ko" Suka fice, duk ina ganin komai na ƙanƙance idona duk ina kallonsu. Hama da Hamma ne suka rage a tsaye ta cika ta batse fam kallonshi tayi tace. "Kana nufin a nan zaka kwana kenan alhalin kasan kwananane yau. Sannan kasan yaufa na dawo duk yadda kake cewa kayi kewata haka zakayi mun?" Ta ƙarashe maganar tana huci. Kallonta yayi ranshi a ɓace yace. "Amman ba zaki tausayama halin da Jabu take ciki ba? Firgita fa take yi kina gani a gabanki fa na yafa mata ruwa ta farfaɗo zan tafi in barta a wannan halinne ga juna biyu a jikinta? Kuma a gabanki Dada tace ke kiyi haƙuri lalurace kema inya kamaki na tabbatar Jabu zata iya bar miki kwananta. Me yasa kike haka?" Tsaki ta doka tace. "Munafurcin banza da wofi, akanta aka soma juna biyu ne Hamma, ko ba haihuwata uku da kaiba. Nii ban taɓa gani ko a cikina na fari kayo haka ba. Shikenan tunda abun rashin adalcine" Ta fice fuu. Ni dai inata nunfarfashi, ban buɗe idanuna ba saida naji Yaya Hamma ya tattagoni ya rungumeni yana shafar kaina yana mun karatu a kunnena" Lumshe idanuna nayi a raina nace kyaji in da daɗi ni da kikai mun a daren amarcina inaji ina gani. Rama cuta ga macuci ibadane" A wannan dare ni dai dangane da matsalar dake damuna akwai sauƙi da canji gaskiya. Sai tambotsai da na dinga yima Hamma duk ya fice a hayyacinshi yanata faman yi mun sannu. Karku mance banci abinci ba, wajajen ɗaya na dare sai nayi kamar irin abun ya lafa na laɓe a jikinshi da sanyin murya nace. Yaya Hamma yinwa nake ji sosai" Zaburar da yayi wajen tambayata abinda zanci saida ya bani tausayi na kanne nace. Sha'awar taliyar Hausa nake ji ta manja da ɗanyan kifi" Ba shiri ya zare idanu yana kallona. "Yanzu ina za'a samu kifi ɗanye Jabu? Taliyar Hausa dai naga Hama ta tawo dashi a cikin garar data dawo dashi, kifinne? Zaki ci haka ba kifin in tasota ta dafa miki?" Ai saina shige jikinshi na saki kukan kissa na sake tashin kanshi. Yaita rarrashi daga baya nace. Haɗa mun tea kawai in sha kawai gobe ka karɓo mun taliyar uwani ta dafa mun" Ajjiyar zuchiya ya sauke ya tashi faka_faka ya hura rushona da bana rabo da kalanzir cike da tanki, bana rabo da kayan tea ma da ɗan kabin biskit ko in mishi sallahun biredi. Tea ya haɗa mun na sha da biskit sannan na kwanta riƙe dashi ƙam. Albishirinku a wannan daren ba ƙaramin bacci mai shegen nauyi nayi ba, dan garin ma saurin waye mun yayi, alhamdulillah sumul nayi baccina. Ai yana tashina da asuba saina zabura na soma rikeshi ina ni karya tafi masallaci tsoro nake ji" "To naji zanyi sallar a gida. Kije ki ɗauro alwala kiyi sallah" Sai dai ai ka rakani, gani nake yi kamar wani abun zai kamani" Dole ƙanwar naƙi ya rakanu banɗaki tare fa muka shiga. Allah cikin amincewarshi muna fitowa muka tarar da Hama a tsaye a gefen banɗakin tana jiran a fito ta shiga bata ma san mu ne a ciki ba. Ga Hamma ya tallafoni hannunshi na ƙuguna ina dai jikinshi sosai. Wani dogon tsaki taja ta wuce banɗaki fu dariya ta kusan suɓucemun na dai kanne da ƙyar. Tare muka yi sallah a takure yana gaba ina bayanshi. Juyowa yayi ya kalleni yace. "Yaya jikin naki, kunje wajen mai maganin kuwa kun karɓo rubutun, ko jikin bai bari kunjeba?" Munje harma nasha nayi hayaƙin duka" Fuskata ya shafa yana murmushi yace. "Jabu nayi matuƙar farin cikin jin labarin cikina da kike ɗauke dashi zaki haihu dani mu sake zamewa abu guda. Ƴan ɓakin ciki su Ummu nabeeha, da M Farida Ammar, da Fadila Abdul, da masu mun fatan maciji ya sareni sai dai su mutu. Amman nasan su Khadija maidoki, Ramlex, A_A nafaɗa, da Mamanmu Hajara duk zasu taya mu murna. Nayi farin ciki sosai Allah yasa ki haifamun aboki da zai dinga tayani kiwo. Sannan ki dinga yin komai a hankali. Tunda Hama ta dawo zata taimaka miki" Idanuna na ƙanƙance nace. Ashe kasan Hama zata dawo jiya amman ni ka kasa sanar mun, baka iya ɓoyema Baɗejo abokinka ba. In ka faɗamun ai ba hanata dawowa zanyi ba face in mata adda'ar dawowa lafiya. Hala shine dalilin da yasa jiya kaƙi sakewa dani abinci ma loma biyu kaya ka ture" Shiru yayi yana kallona. Sai naga ya girgiza kai yana murmushi. "Mata a barku da kishi. Yanzu Jabu fishi kikeyi dan ban faɗa miki dawowar hama ba? Gimbiyar mata aimun afuwa gani a gabanki kuiwa a ƙasa banyi tunanin rashin faɗan zai ɓata miki rai ba" Sai naga ya dena annuri ya ci magani halamar yana son yin magana mai mahimmanci dani. "Jabu jiya a cikin damuwa nake ne. Sakamakon rasa aikina da nayi. Na saba da Alhaji mun kai shekara goma a matsayin masinjanshi, muna tare kuma yana kyautata mun tare da matarshi ma. Wannan shine dalilin da ya hanani sakewa inci abincin. Kuma wallahi Allah shine dalilin daya sha'afar dani wajen faɗa miki Hama zata dawo. Jabu ki yarda ni Hamma san da nake miki in zaki tara mazan duniya wallahi Allah ba zasu miki irin son da nake miki ba. A jiyan damuwace taimun yawa shi yasa" Jikina sai yayi sanyi shi yasa akeson a ko wanne yanayi kaima mutum uziri, sannan ka bashi dama kaji ta bakinshi kafin ka yanke hukuncin da zaka yanke. Meya faru ka rasa aikin ka Yaya Hamma, shine jiya ka ɓoye mun baka sanar dani mun haɗu munyi jimamin tare ba?" Hannayena duka biyu ya riƙe ya fuskanceni sosai. "Ritaya me gidan nawa yayi, zuwa jibi ma zai kwashe iyakinshi ya tattarasu su bar ƙasar baki ɗaya. Kinji abinda ya faru. To sai naga ya dace in mayar da hankalina wajen kiwo, da damuna kuma in yi noman abinda zamu ci a shekara ko da bai kai harda wanda za'a fitar a siyar ba ko? Amman ke meye shawararki?" Kai na girgiza nace. Wannan shawarace mai kyau. Allah sarki Hajiya ashe ƙasar zasu bari to Allah ya haɗasu da mutanen arziki a duk inda zasu koma. Amman ya kamata muje mui musu sallama ko?" Dariya yayi ya sauke ajjiyar zuchiya yace. "Ke da kike fama da rashin lafiya ina ke ina wani fita gari, yadda hanyarmu bata da kyau dinnan ga karamun ciki a jikinki. Ni kaina yau a cikin ɗakinnan zan wuni ina kulawa dake" Idanu na zaro ina mamaki, shi kuma ya soma mun cakulkuli ina dariya ina turmusheshi. Sai ganin Hama mukayi a kanmu. "Ai dama nasan babu ciwon dake damunki. Makirci ne jiya saida kika gama komai naki ni nama dawo gidan bakya nan, kina ganin Hamma kika narke. To ta Allah ba taki ba, kai kuma ka wuce muje ka karya." Murmushi nayi mai cike da kirsa, inna kalleta sai in kalleshi amsar da zai bata nake jira kafin in koreta a ɗakina. "Hama meke damunki haka wai, kar ki bari kishi ya sa ki aikata shirme fa. Kije zanzo inci abincin. Bai kamata kina shigowa ɗakin abokiyar zamanki sasakai haka ba. Musamman in ina ciki gudun kar kiyi gamo da abinda bazai miki daɗin gani ba. Kije ganinan" Ficewa tayi bata tanka ba. Ni kuma saina shiga yi mishi abinda nasan bashi da juriya ta wajen. Fisgoni yayi jikinshi yanai mun raɗa. "Zo muje a bani hakkina tunda abun hakane" Uwar ɗakinmu na labule muka koma anan komai ya gudana cikin soyayya da kwanciyar hankali. Babu abinda ke mun daɗi sama da inga Yaya Hamma ya samu nutsuwarshi dani, kuma a fuskarshi ina ganin farin ciki da annashuwa. Rigarshi ya zura ya fice. Ganin fitarshi, sai matan gidan Yafendo tasa sukaita leƙowa suna gaisheni da jikina harda mazajen nasu. Can sai ga Yafendo da kanta ta shigo da kwano a hannunta cike da farfesun zabuwa ta dure mun. "Jabu Yaya jikin naki da sauƙi ko?' Cikin kunya nace mata da sauƙi miƙewa tayi tace. "To Allah ya ƙara sauƙi ga nama nan ɗan romo romo kisha bakin ki yayi daɗi. Zamu je duba Cubu ni da Baɗɗo. In Yusufu yazo abincinsu yana madafi sai ya ɗauka" Tai mun sallama suka tafi. Suna tafiya na ɗaura ruwan wanka a risho yanayin zafi na juye na je nayo wanka na dawo, na ɗanyi kwalliya mai sauƙi ina zaune na kunna turaren tsinke ya cika ɗakin da ƙamshi sai ga Uwani ta shigo cikin shirin tafiya. "Kaga masu ciki mata a gidan Hamma. Kin haddasa musu fitina gasu can sunata cin uwar sabada muryarsu har tsakar gida. Matan gidanku akwai munafurci duk sun nutsu suna saurarensu ƙauye garin su kare" Dariya nayi muka tafa. Uwani hankali kawai na koya mata matsayina na gwada mata a wajen mijin da take takamar ita ya soma aura. Sannan bansan ta ina zan iya kwana ni ɗaya ba. Uwani Alhamdulillah jiya na samu sauƙi sosai wallahi nayi bacci me kyau yanzu ma ɗakin Baɗɗo nake son inje in sha magungunan. "To Alhamdulillah haka muke so, da izinin Allah wannan dai ya kau. Maza jeki kisha ba'a wasa. Kixo muyi sallama danni zan kama hanya. Na wanke ma Cubu kayanta tas in sun bushe a kai mata. Zuwa nayi ɗakin Baɗɗo na sha rubutu na shafe jikina da tofin da nayi na fito. Har zuwa wannan lokacin Hama sai ihu take harda kuka, Yaya Hamma dai bana jiyo muryarshi. Matan gidan duk sun watse gidan kuwa kamar kitchen ɗin ƙazama sai tarin tulin ƙudaje sunata bin Nono da madarar da suka zuzzubar a ƙasa da kayayyakin da akayi aikin nonon. Farfesun zabonnan na tarar Uwani na ci sanda na shigo. Nima na zuba inaci ina bata labarin yadda muka kwashe daren jiya. Uwani tayi dariya tace. "Ko kefa in ka fiye shiru shiru sai a raina ka. Amman da zaran kana ɗan tabukawa wani abun ma ba za'aima ba. Ya batun siyan kayan mata Iyabo? Akwai mai motar daya shigo damu Girei daga tasha. Ya sanar mun shi ɗan ƙauyannan naku ne wai yaron gidan malam Idi ne mai shanu, ko kun sanshi?" Kai na gyaɗa mata. Na sanshi ƙanin Baɗejo ne. Sunan mahaifinsu kenan" Uwani tace. "To bari Hamma yazo mu tabbatar. Ni da tunanina me zai hana in shi dinne kinga ai gidane, sai in dinga sa lambarshi a jikin kayanki in kaya suka iso Adamawa kinga shi za'a kira yaje ya karɓi kaya. Kinga zai kawo miki har gida. Ke kuma in kaya sun ƙare saiki fita gari kije ki samun kuɗi a banki, zan baki lambar account ɗina. To zamu yi waya kafin ki dawo ƙauyanku ki faɗamun duk abinda kikeso. Naga halama wannan kayan zaki samu alkhairai sosai." Haƙiƙa naji daɗin wannan shawarar taki uwani. Bari Yaya Hamma ya shigo muji. In akwai wasu kuɗaɗen ma a hannunshi zan ara a saro mun kayan da yawa in ajiye kinga guri ba kusa ba" muna cikin tattaunawa Yaya Hamma ya shigo. "Kawayen juna anata hirar ne." Yana daga tsaye a gefe suka gaisa da Uwani. Yaya Hamma. Gidansu Baɗejo shine gidan Modibbo Idi mai Shanu ko?" Kai ya ɗaga mun halamar e, sai na kuma tambayarshi. Suna da ƙani da yake tuƙun mota daga birni zuwa Girai ne Yaya?" "Juma kenan. Me ya faru?" Uwani ta mishi bayanin yadda muka tattauna. Shima yayo na'am da hakan. Nera dubu hamsin na ara a hannun Yaya Hamma munyi zan bashi da zaran na soma saida kaya shi zan soma ware ma kuɗinshi. Na haɗa kan kuɗi masu yawa na ba Uwani. Yaya Hamma ya bata dubu biyar na mota. Tai mana sallama ta tafi da uban man Shanu data siya a hannun Baɗɗo. Haka dai ranar ta zama ta tarihi Yaya Hamma yana gida tare dani, sai jefin azahar sai ga Yafendo da kayan magunguna ta leƙo ta bani tare da yi mun bayanin yadda zanyi amfani dasu. Godiya nayi mata. "Wannan yaro yau baka fita kiwon ba ko? Ka kyauta gara ka zauna ka kula da'ita zuwa gobe ka fita Allah ya ƙara sauƙi" Ni dai babu kunya na ƙunshe Yaya Hamma a ɗaki har sallar Isha a ɗaki yayi ta. A takaice dai sai washe gari Hama ta karɓi miji. Alhamdulillah jikina yayi sauƙi a cikin kwana biyar komai ya zama tarihi, sai ciwon laulayi mai zafi. Duk abinda nasa a bakina sai ya dawo. Madarar shanu kaɗai nake iya sha itace abincina daga tatsota in shata da duminta ko dafawa bana so ayi. Rayuwar tai ta shurawa, makarantata ta sake cika da ɗalibai, cinikin kayan yara har abun mamaki yake bani. Dan cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kayan suka ƙare. Ta bangaren Cubu laulayin nata yayi sauƙi sabida cikin ya tasa. A kullum a hidima nake da Dada duk wani abun daɗi inaba Baɗɗo ta dafa akai mata tai ta sa mun albarka, ga sutura da nake dinka mata. Amaduyal kuwa ya tsaya tsayin daka wajen kulawa da kiwo har duka shanu biyun mata suna ɗauke da juna biyu. Tumakaina kuwa du biyun sun haihu, ɗayar mai laya ta haifi yara uku, ɗayar kuma farar yaro ɗaya ta haifa jal. Haka dai rayuwar tai ta matsawa, ina cikin dangina anata zumunci inata ƙoƙarin yin zumunci dasu. Daso ce sau biyu na taɓa zuwa gidanta, dan ita tana yawan kawo ma Hama ziyara. A haka ne Yafendo ta fahimci kamar Daso ita ke rura wutar rikici a tsakanina da Hama. Sai tai ma tubkaar hanci ta hanyar sanar da Yafendona halin da ake ciki. Ita kuma Yafendo taima Daso tas tunda dama ta san Daso taso Hamma sosai, sai ta saka mata dokar ba zata hanata zuwa gidan ba amman indai tazo iyakarta ɗakin Yafendo. Gaga_gaga anata cuɗa rayuwar. Yau kwanciyar hankali, gobe akasin haka. MRS BUKHARI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (14) Hama irin kishiyoyinnane marasa dadin kishi. Gata da masifar bin bokaye. Duk tabi ta tashi hankalinta akan cikin dake jikina. Wata rana da rikici ya haɗamu har cewa tayi in sha Allah sai cikin ya zama ajalina in mutu uban kowa ya huta. Wannan furucin nata ya haifar mata da fishin Yafendo da Hamma daya ƙwallafa ranshi akan cikin. Yaya Hamma ya fi sati yana fishi da'ita. Ni ko ko a jikina domin da Allah kaɗai na dogara. Kuma Hamma na zuwa wannan ƙauye wajen wannan malami yana karɓomun tofi ina sha ina shafewa a jikina duk daren Allah. Kasuwancin saida magungunan mata ya amsheni sosai a gaskiya. Sai kwana biyunnan dana lodo kaya sai naga yaƙi tafiya an barni da tulin kaya abinda bai taɓa faruwa ba. Abu kamar wasa ya zamana duk abinda na siyo saidai in yi asararshi. Hatta dilar kaya dana sake kuncewa wallahi sai kano na mayar ma Uwani da kayan banda asarar da nayi, ku har man shanu nake tarawa ranar kasuwa in kai ko za'a siya. Ba'a siya sai kace wacce ta kaɗe baƙar karya da baƙar mota. Sau biyu naje, zuwa na biyu harda kindirmon Nono naje mai kyau samanshi harda fatar mai kwance. Yaya Hamma bai ma fa san naje ba. Allah cikin ikonshi yadda na kai haka na jawo tsumman ƙafafuwana na dawo gida, abun bana lafiya bane A cikin watanni biyu da rabi saida na dawo nera biyar tawa wallahi bani da'ita babu da abinda na tsira sai shanu da awakaina wanda su kansu Amaduyal yace du basu da lafiya. Tunkiyata ma kasawa ta kusan yi aka saidata nera dubu takwas. Duka kuɗin na danƙama Dada nace ta ɗan dinga zara tana kashewa. Abinci dai suna samu tunda dama bani ke siya ba, ƙannena nice na zame musu makwafin Dada, dan sai ayi abu a cinye ma bamu faɗa mata ba, kanmu a mugun haɗe yake ga soyayyar juna. Abincin garata ya ƙare, zara bata barin dami. abincin mu kuma a ɗakin Hama yake kullum naje diba saita farfaɗamun maganganu da gorin abincin da nake bawa su Dada. Bana ko tankata ni takaina nake yi kuma da Allah na dogara. Yaya Hamma na roƙa ya gina mana rumbun da za'a dinga ajjiye abincin a ciki, banda rumbun iri da suke ajjiyewa, da buhunhunan masara. Allah ya taimakeni kuwa ya gina, sai na huta da hayagagar Hama. Sai dai tamun akan abinci da nake dafawa in kai gida. Da cikina ya kai wata huɗu ranar talata ranar awo kenan saina tambayi Yaya Hamma inaso in soma zuwa awo tunda cikina ya soma motsi, dake a ɗakina yake ranar, yana shirin zuwa gonane damina ta soma har an soma share gonakai ana jiran ruwa ya tsaya a soma zuba iri. Ya ɗakko nera ɗari biyar ya bani. "Kin ganta ita kaɗai ce a hannuna kiyi maneji dashi har kije ki dawo. Kudin cefanen da zan baki ma wallahi bani dashi dama ɗari biyar ɗince kaɗai ta rage mun." Murmushi nayi mishi nace. Dukkan tsanani yana tare da sauƙi. In sha Allah da zaran na haihu nima sai in dinga ɗaukar tallar nonon ina bin Baɗɗo muna tafiya. Babu komai" Wasu hawayene suka gangaromun da gudu, a hakan ma ina fatan inna ɗauki nonon a siya. Duk abinda na taɓa lalacewa yake yi. Hatta koyar da ɗalibai na sauke ma kaina, da ɗaya da ɗaya suka dena zuwa. Ashe camfani akayi a ƙauyen kunsan ƙauya da camfe camfe wai ni mai rariyar hannu ce. Da naji ragowar ɗaliban da basu dena zuwa ba saina sallamesu. "Ki dena kuka Jabu. Ba zata kai ga haka ba. Akwai alƙawarin dana ɗaukar miki da kikace mun kina da sharaɗi ke ba zaki yi tallar Nono ba. Ni kuma na ɗauki wannan alƙawarin. Daga gona zan shiga gari neman abunyi in sha Allah za'a dace ko na cefanan kwananki ake samu ina laifi" Kafin in tafi awonnan nayi kukan da har saida idanuna suka kumbura. Yafendo naima sallama na fita. Kai tsaye gidan Dada na zarce naje ɗaukar Hassana tai mun rakiya. Dada ta ɗakko ɗari uku ta miƙo mun" A'a Dada ni ban baki ba sai kece zaki ban in karɓa" Kallon tausayi tai mun tace. "Babu komai Jabu karɓi" Godiya nayi mata. Har munje ƙofar gida tace. "Jabu. Amaduyal ya sanar dake halin da ake ciki kuwa akan kiwonki kuwa?" Gabana ya faɗi, a raunace nace. A'a Dada wani abune" "Kuje in kunje kafin ki wuce gida kizo ina nemanki zamu yi wata magana" To Kawai nace mata muka kama hanyar asibiti. Mun sha gwajab_gwalab haka dai muka isa. Layin mata masu awo har bakin babban asibitin Girei mai suna. Girei teaching hospital. A lokacin kyauta ake raba kati komai ma daya shafi awo kyauta akeyi. Domin a hakanma ba wani zuwa asibitin daga cikin ƙauyuka akeyi ba. Sun gwammaci mace taita nakudarta har ta mutu ma akan su kawota asibiti. Ni dai ina zaune akan layi na yi tagumi ina tunanin rayuwa da irin halin da nake ciki. Sauƙina ɗaya babu abinda har yanzu ya canja daga so da kulawar da Yaya Hamma yake mun. Saima abinda yaci gaba, kullum a cikin rarrashina da ban baki yake. Ga rai daya ɗauka yasa akan wannan cikin nawa. Ɗan murmushi nayi na shafi cikin nawa daya fito sosai kamar wanda ya kai wata shida. Yanayin yana mun kama da yanayin cikinsu Taye da Kahinde. Sai wajen azahar aka kira sunana na bi matar data kira sunana a baya, ta bani roba naje nayo fitsari na dawo mata dashi. "Malama Jabu ai babu ciki a tattare dake. A text ɗin da mu ka yi miki na fitsari bai nuna mana kina da juna biyu ba. Amman bari mu miki text ɗin jini." Take jikina ya soma rawa zufa na keto mun. Ga motsin ɗa a cikina amman ace bani da ciki, ga ciki ƙato? Allah cikin ikonshi wallahi anyi text ɗin jini maganar ɗaya ce ciki dai babu shi. Sai janaral asibiti Adamawa suka turani jibi inje za'aimun sikainin. Ta yi rubutu a wata takadda ta bani. Da ƙyar na tashi na fito, cike nake da mamaki, fargaba da tsoro duka dai. Amman in naji motsin rai a cikina sai inga kamar dai basu iya aikinsu bane. Anan Girai na sai kayan miya, da kuka, da maggi. Muka hau akori kura zuwa Jabbi lamba. Gidan Dada muka shiga da sallama Amaduyal ma yana ciki da kuɗi a hannunshi yana ƙirgawa ga wasu ma a hannun Dada. "Adda kun dawo" Cewar Amaduyal. Wani yawo mai kauri na hadiya, da ƙyar nace. Mun dawo Amaduyal yau baka je kiwon ba?" Shiru yayi baice komai ba. Hassana ɗebo mun ruwa in sha ƙishi nake ji" Hassana ta kawo mun ruwa mai sanyi cikin kofi na shanye, Dada sai kallona take a mugun firgice nake. "Lafiya Jabu akwai wata matsalar ne?" A'a Dada gajiyace da rashin kyan hanya ya galabaitar dani" Yanayinta bai nuna ta aminta da abinda nace ba,ta dai mun sannu, kafin tace. "Jabu kinga wannan kuɗaɗe dubu ɗari biyu da sittin gasu. Kuɗin shanunki da awakanki ne. Kinga ga kaji can a bawo guda huɗu nasa an yanka su dan ko ba'a yanka ba mutuwa zasu yi. Ungo wannan kuɗin riƙe" Hannu nasa na amshi kuɗin ina murmushi kawai. "Jabu kisan kadarar da zaki siya ki ajjiye kar ki bari kuɗinnan ya lalace su kaɗai suka rage miki. Sannan inaso ki zama mace mai juriya da jajircewa, ki yarda Allah shi kaɗai yake iya ɗaurama bawa kaddara me kyau da marar kyau. Wata rana zaki huta. Kamar yadda kika sha wahala ni kika fitar dani a matsala. Kema in sha Allah zaki haifi waɗanda zasu fitar dake a matsala. Duk runtsi kar ki rabu da Hamma. Hamma yana sonki kuma zai iya zame miki garkuwa ko bayan raina. Kiyi haƙuri kar ki zargi kishiyarki hakan kar yasa ko bayan raina ki aikata mata wani abun a matsayin ramuwar gayya. Da sannu zata gurbe duk abinda ta shuka. Akan Hamma duk take wannan burinta ta fitar dake a ɗakinki. Ke kuma ki nuna mata kina ma Hamma son da sai dai mutuwa ta rabaku" Hawayen dake zuba a idona na share. Babu komai Dada, na kuma gode da wannan shawarar. Amman inaso zan ba Amaduyal ko da jari ne ya nemi wata sana'ar a cikin wannan kuɗin." "A.a riƙe kuɗinki ki nemi kadara ki siya. Zai yi noma kuma ya samu aikin tuƙa babur zai dinga jigilar shigar da mutane ƙauyuka" Kuɗin na raba Uku na miƙa ma Dada fur taƙi karɓa, haka dole na haƙura na saka kuɗin a jakata. Na zari wasu daga ciki na ba Hassana tamun cefanan tumaturi ta auno mun shinkafar Hausa da Maggi. Suma su Dada nai musu cefane nace su yi girki na basu kaji biyu. Hassana ta rakani har gida da kayan cefanan. Ina tafe kamar mahaukaciya har gidan namu na wuce tafiya fa kawai nake yi, sai da Hassana tace. "Adda kin wuce gidan fa" Kana na juyo naga zahiri na wuce gidan. Da Sallama a bakina na shiga gidan. Yafendo tana tsakar gida, ita da Yafendo A'i. "Jabu kin dawo" Cewar Yafendo A'i. Wajensu na nufa na zube a gabansu muka gaisa. "Ai ɗazu mun shiga wajen Adda Daso ma take sanar mana siyar da dabbobinki da akayi basu da lafiya. Allah yasa da abinda suka tare. Kinsan ba kowa kiwo ya karɓaba shi yasa. Naji kuma sana'ar taki ma jarin duk ya karye miki shima. Jabu kiyi haƙuri jarabawace. Allah daya baki shi zai kuma baki wani, ki ɗau dangana." Suka haɗu sukaita ƙarfafani sai na ji sanyi a raina. A ɗakin Yafendo ma nayi Sallah na kwanta a ƙasa sanyin na mun daɗi. "Ga madarar shanu ɗazu na tatso miki" Yafendo ta miƙo mun na karba ina sha suna hirarsu da fullanci. Allah yayi mun ƙwaƙwalwar saurin jin yare gaskiya. A halin yanzu abu ɗaɗɗayane suke faɗa wanda bana ganewa. Mayarwar ma inayi amman ba sosai ba dai. Sai da nayi la'asar na shiga ɗakina na gyara tas na fito. Kara naje nayo na hura wuta na wanke kajinnan tas na ɗaura a wuta. Na ɗakko dutsen niƙa na gwafe naita niƙa tumaurinnan dasu attaruhu nafi awa ɗaya ina abu ɗaya. Ni kaɗaice a gidan Yafendo ta tafi raka Yafendo A'i zuwa gidan Baffa Musa, daga can zasu je gidan Yafendona. Ni dai inata aiki jikina sukuku. Masu tallar nono an dawo sun sameni na gama suyar kaza na zuba a jar miya ina soya miyar. Ga shinkafa ina zaune inata tsinta da akwai ƙasa sosai. "Kun dawo sannunku" Safiya da Baɗɗo ne dama kaɗai suke amsa sannu da zuwa in nayi musu. Ni dai inata aikina bayana da wuyana duk yabi ya riƙe gam. Sai magriba na wanke shinkafar na zuba. Naje nayo wanka nayi Sallah. Ina idar da Sallah na fito na raba abinci. Ɗaki_ɗaki saida na zuba ma kowa dake shinkafa abun ɗaukanice barinma mai miya da nama. Ina ɗaki shiru ina sauraren motsin da cikina yake yi, idanuna a lumshe ina mamakin yama za'ace anyi awo bani da ciki. To in hakanne meye a cikina yake motsi? Shigowar Yaya Hamma ne yasa na buɗe idona na yi saurin karɓar ledar hannunshi. Kayan miyane a ciki da maggi. Sannu da zuwa Yaya Hamma ya aikin. Wanka zaka soma ko cin abinci?" Zama yayi a ƙasa ya jingina da kujera yace. "Yaya jiki_jikin. Kin ga likita da kuka je asibitin?" Sai gabana ya faɗi. Amman saina jure nace. Naga likita yaronka yana cikin ƙoshin lafiya" murmushi yayi yace. "Allahu ya rabaku lafiya. Allah ya baki lafiya. Bari in soma wankan inzo in baki labari" Ruwan wankan naje na juyo mishi na dawo. Saina ga jini digo uku a ƙofar ɗakina. Gabana ya yanke ya faɗi wata fitinar ce kuma ake so in taka kenan? Cikin gida na shiga na ɗakko tsintsiyar sharar tsakar gida da ragowar ruwan Baɗɗo dana gani a bokiti nazo da bismillah a bakina na wanke jinin tas, nayi adda'a na shige ɗaki ina mamaki. Ina zuba mana abinci Yaya Hamma ya shigo ganin shinkafa da miya harda kaji yasa ya zauna yana kallona. "A ina kika samu kuɗi haka Jabu?" Murmushi nayi mishi kawai nace. Kai dai kaci zan maka bayani " "A'a aimun bayanin tukunna dai. Kaddai zuwa kika yi kika ari kuɗi Jabu. Nasanki dai akwai ɓoye sirri bana jinki" Da dai naga ya fara zargi saina sanar mishi abinda ake ciki. Na ɗaura da cewa. Kuɗin yana jakata na adanasu. Amman dan Allah inaso sati mai zuwa ka yarje mun in je Kano. Inaso zan kaima su Iyaa Debisi ziyara, da Uwani" Shiru yayi kawai yana kallona irin kallon tausayi. Murmushi kawai nake yi dan murmushin yana kwarara mun zuchiyata. "Allah yayi miki albarka. In sha Allah Jabu zan riƙeki da amana ni dai nayi miki alƙawarin ba zaki yi kuka dani ba. Batun zuwa Kano bazan hanaki ba. In lokacin yayi ki shirya kije. Amman meye tunaninki akan kuɗin me kike ganin zaki yi wanda kuɗin bazai rushe ba?" To ka soma cin abincin tukunna muna hirar." Yana cin abinci yana santi, ina mishi dariya. In ina tare dashi yaye mun dukkannun damuwata yake yi. In ina farin ciki mancewa nake yi ina da damuww ma a rayuwa. Gida nake so in siya ko me ɗaki biyu ne a zuba mun haya. Kasan ina da gidan dana siya a kusa da gidan Uwani, da ƴan haya ma a ciki. To ko ta kusa dasu na kuma samu sai in siya, ko kuma in sai fili" Saida ya cika tsokar nama a bakinshi yace. "Allah sarki bansan kina da gida a Kano ba yaushe kika siya?" Bayan aurenmu. Lokacin dana shiga kano A wannan lokacin Uwani taimun tayin wajen saina siya" Kai ya girgiza yace. "To ki sake siyan gidan ko filin kadarace babba musamman dake a birni ne, ba kamar ƙauye ba. Ga kayan miya na siyo miki. Na fita yau da ƙafar dama. Na samu gadi a gidan wani Alhaji a Girei. Daga takwas na safe zuwa shidan yamma zan dinga tafiya. Akwai wanda yake yin na kwana. Duk da nima yace inta kama zan dinga kwanan. Nera dubu huɗu a wata" Nan na shiga murna tare da yi mishi adda'a. Da ƙyar naci naman kazannan ya zauna a cikina. Da safe da nayi dumame kuma sai naji inaso naci da yawa. Da Yaya Hamma zai fita na zari dubu Hamsin na miƙa mishi a hannunshi. Ya kalli kuɗin ya dubeni yace. "Me za'ayi miki dashi?" Nakane na baka kayi noma dashi. Dan girman Allah kar kace mun ba zaka karɓa ba. Dan girman Allah Yaya Hamma" Murmushi yayi yace. "Nagode Allah yayi miki albarka" Ameen ko kai fa. Gobe ance in koma asibiti akwai gwaji da zasu sake yi mun. Nasan inka koma ɗakin uwargidanka bazan ganka ta daɗi ba." Dariya yayi tare da girgiza kanshi yace. "Allah ya nuna mana goben lafiya. Sai mu fita tare ai, ni in wuce aiki ke ki wuce asibiti." Hakan kuwa akayi Bakwai ma mun fice a gidan, har bakin asibiti ya rakani, ya wuce wajen aikinshi. Da naga ya ƙule na fito nayo babban titi na hau mota zuwa gari. Allahu Akbar a babban asibitin ma magana ɗaya ce anyi duk gwaje_gwaje, da hoto, da sikainin amman basu ga komai ba. A zahiri ga ciki sun shaida kuma yana motsi, amman a awo babu ciki babu dalilinshi. Tunda uwata tai sanadin zuwana duniya ban taɓa ji ko ganin abun almara irin wannan ba. Halin dana shiga ya wuce gaban misalin da za'a musalta har ƙwaƙwalwar mai karatu ta ɗauka. Ku kwatanta da kanku, in kece wanne irin ruɗu zaki shiga? To irinshi na shiga nima. Gaga_gaga na dawo gida. Na ja bakina nayi gum babu wanda yasan halin da nake ciki. Ai saina dena bacci, nice sallar dare, nice sadaka. Ko aikin girki nake bana rabo da ambaton Allah. Salatin annabi kuwa sai inyi a rana fin dubu biyu. Da sati ya cika na shirya kayana a akwati na fito naima matan gida sallamar zanje ganin gida. Da ƴar tsarabata a buhu harda nono a jarka, da man shanu duka dai wata tsaraba data dace. Yaya Hamma bai bar tasha ba har saida motarmu ta bar tashar. Ko dana juya baya ina hangoshi ta tangaran ɗin motar yana ma motarmu odabo. Wasu siraran hawayene suka sulalo a kumatuna, a hankali na lumshe idanuna, inata tunano abubbuwan da sukaita faruwa, lallai in haka kishiya take irin hama kishiya bala'ice, masifa ce. Hama ta wargaza mun dukkannin farin cikina, ta hanani sakewa da masoyina sam. Bata ƙaunar a zauna lafiya, in bata zageni, ko taci mun zarafi ba bata samun kwanciyar hankali. Amman ina tausayin ranar da zata soma girbe abinda ta shuka, ranar da zata zama abun tausayi. Dan ƙarshen mai biye_biyen bokaye ba ƙarshe bane me kyau. Macen data mutu akan wannan Gwadaben bata ba shiga aljanna, ba faɗata bace faɗar Allah subhanahu wata'ala ne. ( Jan kunne. Yake ƴar uwata ki sani bin bokaye shirkace. Allah baya gafartama wanda ya mutu yana shirka, kuma babu shi babu jin ƙamshin aljanna. Shin akan ɗa namiji kike son kai kanki ga halaka, kina mace kina zaluntar ƴar uwarki mace? Mace ta haukata kishiya, ta kashe kishiya, ta kashe yaran kishiya, ko ta kassara rayuwarsu. Sai kace munzo duniyane domun mu tabbata. Da muna tuna Allah, da azabobubshi, da muna tuna juma'ar da bata da ƙarshe, da muna tuna wuta, mu tuna aljanna wallahil azeem wasu abun ba zamu yi ba. Ke kina nan kina tabkama kishiya asiri, wata ƙila rayuwarki ma ba mai tsayi bace kije ki faɗi ki mutu Shikenan kin gama yawo. A duniya ba riba, a lahira ba riba, kizo a banza ki koma a wofi. Allah ya ƙara tsare imaninmu ameen) Bayan la'asar muka shiga kano Shigata kano ya famamun ciwukan da har abada ba zasu warke a rayuwata ba. Allah sarki Gwadabe alkhairin Allah ya kai muku tare da yarana a duk inda kuke. Allah ya wadataka ya horema samun macen data kere Iyabo ta kuma" Ni dai kai tsaye gidan Tabalbalin na wuce, nafiso saina gama da harkar asibiti kafin inje gida, kwana biyu rak zanyi a gida in koma. A shago na tadda Uwani tanata cinikayya da mata, ta buɗe dilar kayan jirarirai. Ga Hafizu a cikin shagon yanata rataye wasu kayayyaki a hanga. Shagon an sake gyarashi yayi kyau har doguwar kujera aka saka an sake yawan kantocin, an yi sabon fenti. Acaɓana na ajjiyeni a bakin shagon Hafizu ya iso ya sauke mun buhun kayana, da fantimoti na. "Alaja kece a tafe, maraba" Cewar Hafizu. Murmushi na kakaro nace. Wallahi nice Hafizu nace mutuniyar kwana biyu shiru ni bari in leko. An wuni lafiya ya Amarya da yarinyarta ko yarone?" Baki ya washe. "Duk kowa yana lafiya, ai tama haihu jiya Wallahi an samu Uwani" Baki na kuma washewa. Saida na sallami mai acaɓa nace. Ah ka kyauta. Uwani muka samu, wannan yarinya kace mafaɗaciyace" Tare muka shiga shagon na Uwani, ta ko haɗe rai tamau. Ni nasan bazai wuce akan sunanta da akasa bane, ga cikinta ya fito sosai itama. "Iyabo maraba. Jiya fa nayi mafarkinki kuma wallahi marar daɗi harma nayi sadakar ƙosai mai zafi. Ga waje ki zauna a karɓo miki lemo" Waje ta nuna mun na zauna. Ta ba Hafizu kuɗi ya siyo mun lemo da sakwara. Hmmm Uwani damuwoyi sun yi mun yawa a kannan nawa. Ina tsoron kar in faɗi in mutu mutuwar farar ɗaya. A baya matsalata uwar mijice, sai facaloli. A yanzu matsalata Hama ce, haɗa miji da mace mai asiri bala,ine. Ni wallahi har gara in haɗa miji da makira. Ita duka biyu ta haɗa Uwani. Jibi ga ciki a jikina ga motsi, kuma yana girma. Amman gwajin duniya Uwani likitoci basu ga wannan ciki ba wai babu komai fa a cikin. Kaina ya ɗaure, bacci wannan bana iyawa. Banda bala'e_ bala'en daketa sauka akan dukiyata. To ta faru ma ta ƙare tunda yanzu komai nawa ya ƙare tas" Hawaye na sharce bayan na ƙarashe maganata. Uwani kuwa kasaƙe tayi tana kallona kawai. "Iyabo na shiga uku. Wannan tashin hankali har ina. Babu ciki likitoci basu ga cikin ba kikace. To mijin naki wanne mataki ya ɗauka akan hakan? Kinga jikina rawa yake yi Iyabo" Hamma baisan abinda ake ciki ba sam. Na ɓoye mishi Uwani kar kiso ganin yadda ya ɗauki rai ya ƙallafa akan wannan ciki. Shi burinshi ya haɗa jini dani Uwani. Wallahi tsoro da fargabar me kaje kazo ne ya hanani ce mishi komai. Ina cikin tsaka mai wahalar fita." Kuka na fashe dashi, nayi shi ƙaƙas sai naji zuchiyata ta ɗan rage naunyi ni da kaina nayi shiru. Uwani bata hanani kuka ba. A ko da yaushe Uwani takance kuka shima wata hanyace ta rage nauyin zuchiya da cunkushewarta. "Hmmmm ki kwantar da hankalinki Iyabo. Zamu zagaye asibitocin Kano. Kuma in sha Allah za'a dace. Akwai wani malami zan ɗaukeki muje zai taimaka miki." Dawowar Hafizu ne ya katse mana hirarmu. Lemon montin dew ya ajjiye a gabana. Da kular sakwara. "Hajiya tunda kinyi baƙuwa zan tafi. Sannan ki daure kije ki duba me jego da takwararki" Uwani ta dubeshi sai naga tayi dariya, ta zuge lalita ta ciro kuɗi ta bashi. "Ga albashinka nan" Yayi saurin cewa.." "A'a ki riƙe a wajenki. A tsintamun kayan jaririya a cikin kwashe irin na ɗari_ɗari ko tsinke ban siya ba" Kuɗin Uwani ta mayar tace. "Gasu can ƴan ɗari_ɗarin ka ɗebi na iya kuɗinka" Ni dai ina jinsu, Sakwara nake ci hannu baka hannu ƙwarya ga ganda sutu_sutu a miyar. Sai da Hafizu ya fita nace. Uwani ki ƙyale Hafizu haka dan Allah " "A'a fa Iyabo. Barni da Hafizu inda kika gammu. Nifa a haka nayi matuƙar ƙoƙari da kai zuchiyata nesa tunda har na iya ɗaukarshi aiki nake biyanshi duk sati yake samun naci da iyalinshi. Banyi ƙoƙari bane nifa nake ci da kaina da nawa yaran. A shago ina siya mai abincin rana. To me kike so, in goyashi in yi yawo dashi kome? Kinfa san komai duk ba akan Hafizu naje na afka bala'in da Allah ne yayi ina da tsayin rayuwa ba. A ƙarshe me yayi mun?" Anan zan dakata sai ranar monday kuma MRS BUKHARI Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/IW4UEOnp70d9ho1A7dH1Ba Kina son yin adashen kayan Sallah daga wajen Anty Zee misa colaction? Ga link maza ki garzaya kema ayi dake tana kawo kayayyakinta daga ƙashashe daban_daban masu inganci da rahusa. Nima a wajenta zanyi adashen kayan Sallah na. Ina masoyana kui maza ku shiga ayi daku NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (15) "Ba aure yayo da kuɗinshi ba, abinda yayi ragowa ya cinye shi da amaryarshi ba? Wai ko so kike in danƙa mishi ragamar dukiyata ne, sai yadda yayi da'ita?" Tabalbalin ta dinga faɗa ta inda take shiga ba tanan take ɓullowaba. Ni dai dana gama cin sakwara saina miƙe. Bari in shiga ciki in ɗauro alwala inzo in yi sallah" Ciki na shiga na kama ruwa nai alwala. Sai kawai ma nayi sallata tunda yaran suna ciki sai murnar ganina suke yi. Fitowa nayi shago na tarar da wata mata suna maganar filaye da Uwani. "Kinga filin yayi sauƙi manyane dubu ɗari_ɗari aketa yankawa wallahi nan da shekara biyar wajannan cika zaiyi sosai. Shi yasa nace bari in sanar miki ko kina da buƙata ƙanina ne suke yanka wajan" Cewar wannan Mata kenan. Uwani tace. "To zan duba kuɗaɗen wajena, ko kuma zuwa karshen mako akwai dashi da zan ɗauka kuma da kauri ko guda biyu ne sai in siya in haɗe ai" Ai sai nayi carab nace. In babu matsala Uwani nima ai sai in siya tunda na siyar da shanuna kiwon yaƙi sai ciwo suke yi" Baki Uwani ta riƙe cike da mamaki. Numfashi ta sauke tace. "To babu damuwa Halima da daddare zamu zo in Bellon ya dawo sai muyi magana ƙawata zata siya. Wannan ƙawatace tun muna yara tare muka je saudiyya da'ita. Zan siya sai a bamu kusa da juna" Da wannan matar tai mana sallama akan sai ta ganmu zuwa daren. "Wai kiwon ma Hama ta hanaki kiyi sabida bata son kiyi arziki? Hmmm kingani ko Iyabo kinsan muguntar mutumin ƙauye kuwa? Yanzu da ba dan kina da wannan gidan ba da haka kuɗin zasu haɗu su galgance jibi asarori da kika tabka. Ni da ace iyakar karayar jarine da yanzu na ɗoraki da yardar Allah. To ba'a siyan komai ne a hannunki baƙin asiri mitsiyaciyar tayi miki na baƙin jini. To ince dai bata da labarin gidan da kike dashi ko?" Bata da labari, ko shi Hamma bai jima da sani ba. Hatta su Dada babu wanda yasan ina da gidannan. Wannan kuɗin dabbobinne ma Dada tace in samu in mallaki kadara. To Uwani kina ganin ko in siyar da ɗan kunne da sarkar da Saleem ya bani da wanda na siya a siya mun gida a sake zuba ƴan haya. Amman ke me kika gani. Inata ajjiye dasu su ba kawo mun kuɗi suke yi ba, ko babu komai hayar zatai mun amfani zan dinga karɓar kuɗina ina magance ƴan matsalolina. Amman meye shawararki?" Uwani tayi jim tace. "Magana ta domin Allah in kin tawo dasu ai gara a haɗa a siyar dukka, mu haɗa da ƴan kuɗaɗen dake jikinki, shima wannan gidan a siyar sai a sai babba ko da gidan samane, me ɗakuna da yawa. Kinga duk shekara zaki samu kuɗaɗe masu kauri a hannunki, zakita jalautawa. A ƙauye in kinsa zinare ma waya sani babu. Ai gara ace ƙasa gareki itace babbar kadarar da babu asara a cikinta, yaranki ma sai su gada duk da dai fulanin gadon shanayen wahala ake bar musu" Mun jima muna tattsunawa. Dab magriba Uwani ta kulle shagonta muka shiga ciki. Tuwo ta tuƙa mana dama tayi miyarta ta ɗanyen karkashi yaji ɗanyan kifi tun safe, ga yajin daddawa mai daɗi da take siyarwa, ga man shanu shima soyayye da take siyarwa. Uwani fa ƙaƙas ta zama ƴar kasuwa. Bayan munyi Sallah muka ci tuwonmu munata hira, sai naji rabi da kwatan matsalata kamar ta kau. Sai da mu kai Isha Uwani ta ɗebi kayan jajirai muka tafi gidan kishiyarta barka. Gidan duk ya fice a hayyacinshi yayi biji, biji. Da Sallama muka shiga ɗakin. Jaririyar sai kuka take canyarawa. Ashe ba kowa ne a ɗakin, ko ina uwar oho sai wan jaririyar yana zaune da ƙaton ciki sai gyangyaɗi yake yi. Uwani tayi haka zata ɗauko jaririyar a gado mai rumfa. Uwar jaririyar ta shigo da gudu ta riga Uwani ɗaukarta. Har tana sauke ajjiyar zuchiya. Wai ashe haka kishi, da kishiya yake?. "Tunda naji kukan yayi yawa nace ko wani abunne mugu ya sameta ashe kune. Sannunku da zuwa" Ta ƙarashe zancan tana dariya. Uwani ta dubeni, ta dubi kishiyar tata tace. "Mune mugayen da muka kusanceta kenan shi yasa take irin wannan kukan? Yayi kyau baki da laifi" "Lahh wallahi Innar Zainab ni ba haka nake nufi ba kar ki juya mun maganata dan Allah" Uwani zata kuma magana na taɓata ta baya. Wannan karon nako ci sa'a sai tayi shiru muka zauna. Ta bamu jaririya taƙi ta ƙanƙameta, daga ƙarshe saita cusama yarinyar mama. Wani shafaffen yanƙwanannen mama. Hafizu ne yayo sallama ya shigo. Ganinmu ne yasa ya washe bakinshi. "Iyabo ashe kun shigo. Ke basu jaririyar ki kawo musu abinci." "Tayi bacci ma" Ta faɗa. Uwani tayi dariya tace. "Kinga kwantar da'ita in tayi bacci. Abinci kuma ki bar abinki. Iyabo Jeka lo ( muje)" Miƙewa nayi, ledar dake hannun Uwani saita miƙa ma Hafizu tace. "Ga gumama asa ma takwarata" Ya amsa yanata godiya. Mu dai nan muka fito muka barsu, ya suka ƙare oho musu. Wai Uwani yadda kishiyarki ta ɗaukeki kenan baƙar muguwa? Kinji furucinta wai me yasa kishiyoyin kusan halayyarsu gudane, sai ɗaiɗaiku da suka rabauta?" "Rabu da matsiyaciya. Baƙin ciki nan take Hafizu na aiki a ƙarƙashina, da kuɗina ake ciyar da'ita. Da bini_bini zata biyoshi har shago wai tazo ganinshi. Tasa na sallameshi da ƙyar na dawo dashi, da sharaɗin matarshi karta kuma zuwa nemanshi. Ko gidan biki ko suna haka na maƙota dana shiga sai ta sha jinin jikinta. Ni nafi ƙarfinta da ba dan haka ba wannan ƴar ƙauyan juyanu zata yi kamar waina. Shakkarta fa shi kanshi Hafizun yake yi, damma yasan ba kyau ba daɗi ni ɗin, shima da tsiyar zai tatamun ta su rijalu." Washe gari Sassafe muka wuce asibitin murtala, bayan bin dogon layin awo. Bata fa sauya zani ba, magana guda ɗayace. Bani da ciki su basu ga komai ba. Hankali saiya tashi fiye dana ko yaushe. Danni abinda nasa a raina shine a Adamawa akasi aka samu, bana jin asibitocin Kano indai dan ƙwarewa ne. Munbi asibitin kudi huɗu a ranar wallahi zancan ɗayane. Kafin yamma idanuna ya faɗa na yi wata rama ta fatat ɗaya. "Iyabo gobe zamu buga sammako zuwa lahadin makoli wajen mai maganin dana faɗa miki. Muje da izinin Allah zamu dace, kuma a dage da adda'a " Kayya Uwani, ni ina ganin mu haƙura da zuwa wani gidan magani. A asibiti ba'a gani ba sai a wajen mai maganin hausa ne za'a gani? Allah yana ji yana gani shi zai bani mafita." Uwani ta dafani tace. "Bazan hanaki kuka ba. Wallahi nima dauriyace tasa ban zubar da hawaye ba. Amman fa Iyabo kowa yasai rariya yasan zata zubda ruwa. Ni dake a asibiti muka ga dunƙule magani a cikin abinci. Amman idanki ya rufe Hamma kawai. Alhalin ya kamata ace ki duba waye abokiyar zamanki shima yana da mahimmanci. Matan katsina, Sokoto, zamfara, Maiduguri me yasa zaki ga in akaji dasu za'a haɗa kishi sai kiga an tashi hankali? Sabida waɗannan garuruwa dana lissafa sunyi ƙaurin suna wajen kassara kishiya, da mugun dumi suke ɗaukar sha'anin kishi. ( Kuyi haƙuri ba duka ake nufi ba, mafi yawancin ƴan garuruwan da aka ambata haka suke. Amman akwai da dama waɗanda ba haka suke ba. Kar a mance labarin na gaske ne ba ƙirƙirarshi akayi ba) Iyabo mun kama laya a cikin fulonki, muka so ni da Baɗɗo a nuna ma uwar mijinku. Amman kika ƙi waike kaza ke kaza kar aurenta ya mutu. Ba gara aurenta ya mutu ba akan ta tarwatsa rayuwarki. Zuchiyar bafulatani fa tauri gareta basa jin kira. Yanzu jibi a cikin dare dubu ɗari da ɗayan data saki, baki mutu ba alƙiyamarki ta tsaya. Ga ciki yana motsi, yana girma amman ba ciki bane" Kukana ne ya sake tsananta, ina ganin meye laifi danna zaɓi in rayu da sanyin idaniyata. Soyayyar da nake ma yaya Hamma ta wuce gaban kwatance, dan ko mayyace Hama bazai sa in janye aurenshi ba. Ganin kukana yayi yawa ga dare ya raba Uwani taita rarrashina. A daren ranar bacci banba, ni innaji cikina yayi motsi sai tsoro, dan bansan dame nake rayuwa a ciki ba. Washe gari ni ko wanka banyi ba muka wuce, da ƙyar da suɗin goshi Uwani tasa nasha kokko da ƙosai biyu muka wuce. Motar Karamar hukumar warawa muka shiga, daga warawa muka hau akori kura zuwa Ƙauyan Lahadin makoli. Daga lahadin makolinma saida mu ka yi tafiyar ɗari bibbiyu a Acaɓa. Tafiyar ɗari biyu a ƙauye bafa ƙaramar tafiya bace. Sai gamu a wata bukka da mata masu ciki zuzzube a ƙasa. Wasu cikinsu ya kusan haihuwa, wasu kuma cikin kamar dai nawa, wasu ma cikin bai kai nawa ba. Layi Uwani ta kama mana, muka samu mu kai azahar, ta siya mana ɗanwake da mai da yaji. Ni bakina ma ɗaci yake yi da ƙyar dana sa ɗanwaken a bakina na haɗiye. Uwani dan Allah ki rabu dani da abinci. Ki barni inji da damuwata" Murmushi tayi tace. "Ki yarda da Ubangijin daya kuɓutar dake daga hannun larabawannan da suka nemi ranmu. Ki kuma yarda da ubangijin daya taimakeki kika auri Gwadabe a lokacin da duk wanda ya kalli alaƙar cewa yake bazai yiwu ba. Ki yarda da ubangijin daya ƙadarta miki auren Hamma har kika shiga wannan halin. Ki yarda zaki samu taimako daga gareshi. Iyabo nasanki da tawakkali da ɗaukar komai ba komai ba. Amman naga wannan lamarin kin ɗaukeshi da matuƙar zafi. Kici abinci kar ki kashe kanki" Wallahi maganganun Uwani sai suka wanke mun kai. Wani tawakkali ya sakko mun. Murmushi nayi nasa hannu na karɓi ɗanwaken na cinye tas na sha ruwa. Na dubeta nayi murmushi. Itama murmusawa tayi. A haka har layi yazo kanmu. Mu huɗu muka shiga masu ciki, sai Uwani ta biyar. Ta farkon itace ta soma bayaninta, wanda ya gigita tunanina. "Malam shekarata uku ɗauke da wannan cikin. Ni ban haihu ba, ni ban huta ba Malam. Naje wajen masu magani iri daban_daban amman ba'a dace ba Malam. Kishiyata ce ta biyun taimun baki a lokacin da mijinmu yake rawar ƙafar na samu ciki yana saka ran haifa mishi namiji. Shine tace, in dai tana doron ƙasa ban isa na haife cikinnan ba. Shekaru uku kenan har mijin ma ya gaji ya sakeni, ina gida da ciki" Take zufa ta wankeni, jikina ya shiga ɓari. Malaminne ya soma magana da cewa. "Kwantar da cikin akayi bazai yi gaba ba bazaiyi baya ba. Amman kin kawo kukanki gidan mutuwa Akwai aljanin da zamu sa ya tayar miki da cikin. Zaki kawo baƙin raƙumi, da baƙin bunsuru, da ɓakar tunkiya, da baƙar mage. Wannan shine ladan aikin" Zumbur na miƙe ina haƙi, tari ya kamani na nufi hanyar waje. Uwani ta biyoni tana riƙeni muka fita. Uwani dama kina ta'amali da bokaye ban sani ba muke ta abota?" Na tambayeta raina a ɓace hankalina a tashe. Ita kanta a cikin rudu tace. "Wallahi Allah bansan boka bane. Kinsan Allah da girma yake Iyabo wajannan wata maƙociyatace ta taɓa zuwa, tana neman maganin haihuwa, ita ta kwatanta mun. Barni da Balbalin kema kin sani harkar shirka bana ciki. Mu maza mu bar wajannan danni gabana ma faɗuwa yake yi" Ba shiri mka bar wajen, a ciki na baro takalmina warin ƙafar hagu. Bamu muka koma gida ba sai wajajen sha ɗayan dare wallahi, gajiya, yinwa duk mun kwaso. Ni babbar damuwata bansan ko Allah zai amshi sallolinmu ba. Duk da shine masanin gaibu, munje wajenne ba tare da ilimin boka bane. Ni dai a zarge na rama sallolina. Uwani Allah yana gani zan koma gida muita adda,a da izinin Allah zai mun mafita. Bazan sake zuwa asibiti ko wani maganin gargajiya ba. Lokaci zaiyi halinsa, Allah zai nuna ma Hama ikonshi nayi wannan imanin Allah zai dubeni." Kwanana goma cib a garin Kano. Kwana huɗu a gidan Uwani, kwana shidda a gidanmu. A kwanaki gomannan na siyar da zinaraina, Uwani ta sai gidana dake jikin nata muka gagganɗa kuɗin aka siya mun gidan sama mai ɗakuna goma sha biyar, da shaguna huɗu. Burodami Kokodeen da Burodami Debisi, da Uwani sune suka zama shaiduna, muka biya aka gyara takaddu da cike_ciken abinda ya dace, na kamo hanya na dawo, gida na hannun Uwani da Burodami Debisi su zasu saka haya su amshi kuɗin hayar. Ƴan canjinan da suka ragemun, na siyo kayan aune, aune, da busassun kayan miya, da maggi dunƙule da fari, da dai abinda duk nasan ina buƙata. Iyaa Debisi ma tayi mun tsarabar doya, garin alba, garin amala, bushasshiyar gandane. Burodami Debisi shi kuma shinkafa da wake ya aunarmun mai yawa, ya kawo nama akaimun miyar stew soyayya mara ruwa ƙaramar robar fenti. Uwani kuma kayan miya ta siya da yawa aka niƙo ta tafasamun ta duramun a jarka aka zuba mai a saman, yana daɗewa sosai bai lalace ba. Banda tarkacen su yajin daddawane, jan yaji ne. Tsaraba dai rigi_rigi na koma da'ita. A tasha na samu Yaya Hamma a tsaye kamar yadda ya saba yana jiran dawowata. Da magriba matan gidan duk suna tsakar gida anata aikace_aikace sai gamu mun shigo da sallamata. Ga yara na bina da kaya rigi_rigi. Yaya Hamma shima yana riƙe da wasu kayan. Hmm kunsan me? Da muka gaisa da matan gida saina nufi ɓarayin Yafendo na yada zango acan. Yaya Hamma kuma ya wuce masallaci, dan anata kiraye,kirayen Sallah. Bayan na rama sallolina Baɗɗo ta kawo mun tuwo naci. Sai Yafendo take faɗamun mummunan abinda ya afku bayan kwana uku da tafiyata. "Jabu ai bayan tafiyarki da kwana uku gobara ta tashi a lungunku. Da ɗakin Safiya, da Ɗakin Fatu ƙarama da naki. Ƙurmus suka yi babu abinda aka ɗauka. Gobarar daga ɗakin Fatu ƙarama ta tashi, anyi ruwa mamako saita shiga da gaushi ɗakin. Ashe ya kama zanin gadonta ita bata sani ba, cikin dare sai wuta ta tashi. Murmusawa nayi idona na hawayen da suke shirin makanta ganina nace. Allah yasa sa da abinda ya tare" Yafendo ta girgiza kai tace. "Ameen. Bayin Allah duk sun kakkawo taimako anata kan karɓa kinsan mutanen ƙauye da haɗin kai. Zamu kwana tare dake anan har zuwa a gyara miki ɗakin naki. Su Safiya duk suna gidansu." To Shikenan Yafendo mun gode. Shigowar Yaya Hamma yasa Yafendo ta fice ta bamu waje. Zama yayi yana fuskantata, ni kuma inata share hawayen da nayi yin duniya yaƙi tsaiwa, da kanshi yake hankaɗo kanshi. Kallon tausayi yake yi mun, mai cike da tsantsar so. "Kiyi haƙuri Jabu. Haka Allah ya ƙadarto mana. Daga wannan sai mu faɗa wannan. Aikin gadin dana samu ma ya kuɓuce mun. Matar gidan tasa an ɗakko ɗan uwan mijin a ƙauye an bashi aikin. Shanun da nake gadara dasu duk sun soma ciwo, yanzu haka Yuguda ya tafi dasu asibitin dabbobi. Annobar bace ta samu shanun. Waɗanda shanayensu basu kama ciwo ba, duk sun tafi ciranin dole, dan gujema annobar. To mu kam kusan rabin shanunmu ciwon ya kamasu, jikinsu duk kuraje. Kaɗan daga ciki da basu fi ashirin ba Jumare ya tafi cirani dasu. Kiyi haƙuri zan sai miki kayan ɗaki gwargwadon halina." A'a Yaya Hamma. A halin yanzu bata kayan ɗaki ake ba. Mu yi adda'ar Allah ya kawo sauƙin wannan annoba data samu shanun kawai. Babu komai zamuita lallaɓawa" Jigum_jigum muka yi. Kunsan dai bafulatani da Shanu. Baffa Musa ma ance yana kwance babu yadda yake a dalilin shanayenshi wajen bakwai sun mutu. An siyar da kusan goma. Jikin nashi yayi tsananin tsananta. Haka a daren muka je dubashi baya gane ma wanda yake kanshi. Mu dai gamu jigum_jigum su Dada sai sharar hawaye suke yi. Domin shi suke gani a makwafin uba a garesu. Wannan kenan. Su Yafendo ne suka yanke shawarar data tashi hankalina cewar asubar fari Yaya Hamma ya kora shanun Baffa Musa ya tafi wannan cirani dasu. Ai kuwa hakan akayi, a gidan Baffa Musa dukka muka kwana. Washe gari sassafe gun_gun matasa da magidanta suka haɗe kawunansu suka ɗau hanyar dokar daji, su kansu basusan a ina zasu samu garin da zasu yada zango su kafa tantinsu ba. Har waje nabi Hamma ina kuka. Ku dubi kunya irinta bafulatanin mutum amman gam Yaya Hamma ya riƙe hannayena yace. Har abada soyayyarki ta dabance a zuchiyata bazan mance da halaccinki a gareni ba. Jabu ki tayani da adda'a ba zan fi shekara ɗaya ba ko dan inzo inga abinda kika haifa zan dawo. Bazan mutu ba har sai Allah ya sake ara mana lokacin da zamu sake shinfiɗa sabuwar rayuwa. Yara goma sha biyu zaki haifamun dukka maza in sha Allah." Ina kuka ina murmushi mu kai sallama yabi ayarin gungun fulani da gungun shanaye, suna tafe suna waƙar fullanci ta nuna jarumtarsu. A ranar nayi kuka sosai. Sun tafi babu jimawa dan ko awa uku ba'aiba da tafiyarsu Allah ya ɗauki ram Baffa Musa sanadiyyar mutuwar shanunshi fulani da shanu ba dama ne. A wannan shekarar anyi asarar dukiya anyi asarar rayuka sosai. Dan wasu da kansu suka kashe kansu, wasu kuma zuchiya suka haɗiye suka mutu. Haka akaita zubar da gawawwakin dabbobi abin tausayi. Wasu wannan ne yai silar karayar arzikinsu ciki harda Mijin Cubu, da mai Nagge mahaifinsu Baɗɗo, danshi kab shanunshi wayar gari akayi asa tarar sun mutu. Sai ya zama kamar wani zautacce_zautacce haka. BAYAN WATA UKU Ina zaune a ɗakina da wuta taci aka gyaramun na buga tagumi ina tunanin ko Allah zai sa mu sake ganawa da Yaya Hamma sai Allah. Ga cikina ya girma watanshi kusan takwas da kwana goma sha ɗaya. Yayi girma sosai, kullum fargabata yaya zanyi mu rabu da wannan ciki nake. Ƙila shine ajalina dan inaji a raina kamar ƙarshen rabuwata da yaya Hamma kenan. Yafendo ce ta leƙo. Na ɗago na dubeta. "Jabu kina zaune kina faman aikin tunanin kina da juna biyu? Maza fito ki sha iska ga magani na dafa miki kisha" Da dabara na tashi, dan cikin ya girma sosai. A ƙofar ɗakinta ta shinfiɗamun tabarma na zauna ina haki. Maganin zaƙi ta bani cikin kofi na kafa kai na shanye, kasancewar ba magani mai ɗaci bane. Ta ajjiyemun lafiyayyen Nono yaji dambu shi kaɗai nake iya sha, bana gajiya. Sai in sha sau nawa. Gashi nonon ma wuya yake yi kasancewar babu shanun yanzu. Su Baɗɗo ma sai kwalba da madara suke ma ƴar dabara su fita dashi a matsayin nono, in ba a gabanka akayiba ba ka ce ba Nonon usul bane. Yafendo sai jana da hira take yi har su Baɗɗo suka yo sallama suka shigo. Hama ma cikinta watanshi huɗu a jikinta tana ta dai gwalli ita namiji zata haifama Yaya Hamma daya dawo zai zo ya tarar da abin mamaki. Ni dai dama kunsan a mugun tsorace nake, ku kunsan komai. Cikina a daren daya cika wata tara wajen sha biyun dare ina kwance a kasa a bukkar Yafendo naƙuda ta tashi. Dama kwana biyu dai inajin jikin babu daɗi a tsaitsaye dai nake yi. Gobe ba zaku samu ba yauma dan nayi alƙawarine ayimun afuwa. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (16) MARAƊI:. BAYAN WANI LOKACI.: Abubbuwa da dama sun faffaru a cikin wannan shuɗewar lokaci. Ciki harda rasuwar Balaraba. Ta rasu wajen haihuwane ta haifi ɗiyarta mace sai aka mayar mata da sunan mahaifiyarta. A lokacin Anti Badi'a shayarwa take yi, sai ta ɗauki Balaraba ta haɗa da Saifullah taci gaba da shayar dasu. Duk matan gidan sun ƙara haihuwa banda matar Mammada da ko ɓatan wata bata taɓa yi ba. Hadiza, da matar Sabitu kuma suna turawa haihuwa ko yau ko gobe. Malam ya samu lafiya sosai sai dai Baba Fhatsima tana cikin halin jinya sosai. Watansu kusan uku tana kwance a asibiti cutar ciwon zuchiya take yi. Daga baya Malam yasa aka sallamota suka koma yin na hausa. Ta bangaren Gwadabe sai godiya dan a yanzu in ba'a kirashi hamshaƙi ba a kirashi mai kuɗi. Ya samu rufin asiri sosai da sosai. Ya ɗebo yaranshi ya dawo dasu kusa dashi. Toye yana hannun Hadiza, ƴan biyu kuma suna hannun Shafa dama sun saba. Rayuwa ta warware musu sosai. A ko da yaushe a cikin yi ma Bara'u aike yake. Damunan bana ya taimakama Bara'u da kuɗi yayi noman gyaɗa ya samu albarkar abun sosai da sosai. Wannan kenan Shafa ce tsaye a tsakar ɗakinta tana ta jijjiga yarinyarta mai suna Iyabo yar wata Takwas yarinyar akwaita da kuka, bacci ma basa iyayi. Gashi Allah ya jarabci Shafa da samun wani juna biyun na uku kenan, watan cikin biyu a jikinta sai ɗan karen laulayi ga fitinar Iyabo mai kukan banza. Ƴan biyu ne suka dawo daga makarantar yamma ta malam suna jaye da hannun Abba suka shigo da alawa a hannunsu malam ya basu. Kamar daga sama Shafa ta jiyo kamar Hadiza na ƙwalo mata kira. "Zo ku zauna Toye karku fito. Zanje ɗakin su ummi yanzu zan dawo." Tana gama fadin haka ta fito da sauri. A falo ta samu Hadiza tana murƙususun naƙuda. "Shafa kije ki kira mun Anti Badi'a dan Allah naƙuda nake yi." Da sauri Shafa ta nufi ɓarayin Anti Badi'a ta sanar mata halin da ake ciki. "Abinda za'ayi Shafa ki shiga cikin gida ki karɓo rubutu a wajen Malam sai ki sanar musu halin da ake ciki." Tare suka tawo Shafa ta wuce cikin gida, Anti Badi'a ta shiga wajan mai naƙuda. Ciwon naƙuda har magriba haka su Gwadabe suka dawo suka tadda wannan lamari. Sau uku Malam nayo rubutu Baba Asshi na kawowa abu har bayan isha ana abu ɗaya. Dole aka tafi da Hadiza asibiti a motar Yaya Tasi'u ranga_ranga. Tafiyarsu da kaɗan Allah yai ma Baba Fhatsima cikawa gida ya ruɗe aka fasa kukan mutuwarta. Su Gwadabe suna hanya Malam ya kira Yaya Tasi'u yana shaida mishi halin da ake ciki. Haƙiƙa anyi babban rashi a cikin wannan zuria. Rashin daya taɓa kab ahalin gidan, mutuwar data sauya zukata daga ƙiyayyar juna zuwa haƙuri da dangana. A rayuwa komai yana da mafari, kuma komai yana da ƙarshenshi. Su Yaya Tasi'u suna shiga asibiti aka shige da Hadiza, amman likitoci sun bayar da sanarwar tiyata za'ayi mata. Gwadabe hannunshi na rawa yasa hannu a takaddar amincewa, da gaggawa aka shiga da'ita. Yaya Tasi'u ya matso kusa da Baba Asshi, da Gwadabe, da Anti Badi'a yace. "Allah yayi ma Baba rasuwa muna fitowa. Ɗazu a mota kiran da malam yayi mun kenan. Tata ta ƙare Baba, sauran namu ya rage inma mu haɗe kawunanmu mu zama zuria ɗaya, imma mutuwa tai ta yi mana ɗauki ɗaiɗai" Abun mamaki mutuwar Baba Fhatsima ta jijjiga Baba Asshi dan rikicewa tayi da kuka kamar ba kishiyarta ba. Yaya Tasi'u ya share hawayenshi ya riƙe hannayen Baba asshi yace. "Ki yarda ki zame mana makwafin Baba. Ki amince a kawo ƙarshen wannan tashin hankali mutuwa ci take kamar rana." Baba Asshi yau itace ta sa kanta a ƙirjin Yaya Tasi'u tana kuka. Dukkansu a wajen kuka suke yi. Gwadabe abu ya rikice mishi ya haɗe mishi biyu, ga mata a wani hali, ga suruka kuma uwa ta rasu. Da Yaya Tasi'u da Baba Asshi suka koma gida, akabar gwadabe da Anti Badi'a sunata kaikawo idanunsu jawur kamar garwashi. Sai misalin ƙarfe sha ɗayan dare aka fito da Hadiza daga ɗakin tiyata tare da ɗiyarta macce zuwa ɗakin hutu. A lokacin ne Gwadabe ya samu sassauci daga tashin hankalin da yake ciki. A haka suka yi kwanan zaune asubar fari Gwadabe ya kama hanyar gida. Yaje ya tarar ƙofar gidan Malam dafifin al'umma ne kawai suka cika ƙofar gidan, Malam na da jama'a sosai, haka Baba Fhatsima matace ta mutane kowa nata ne banda ɗan banza. A cikin gidanma cike da mata anata koke_ koke kab yaran gidan sun zo, ko wanne ka kalla yana cikin tashin hankali marar misali mutuwar ta doki waɗanda ma ba,ai zato ba dan a kuka harda su Sabitu sai haƙuri ake bashi. Sabitu a tsakar ɗakin Baba Fhatsima ya gama rarrafenshi, goyo kuwa Tasi'u ne kaɗai ya fishi more bayanta, sai shi yazo a na biyunshi. Gwadabe ya kutsa kai zuwa turakar Malam inda duk yaran gidan suke, matan guda biyu manya suna ciki ana ma Baba Fhatsima sutura. Zama Gwadabe yayi yana sharar hawaye. "Tasi'u kuzo ku fito da makarar zuwa falo kui mata adda'a a kaita makwancinta" Malam fa yana zaune babu yadda yake tsabaragen damuwa, ciwonshi ma tun jiya yayi tsanani ya bari a kaishi asibiti yaƙi yace shi zai sallaci gawar ƴar aljanna, ya sata a kabarinta. Yaya Tasi'u da Gwadabe ne suka fito da gawar suka ajjiye a gaban Malam. Malam ya girgiza kai yace. "Fhatsima Allah ya baki sa'ar tafiya. In dai sai miji ya ɗaga ƙafa ake shigewa aljanna to Fhatsima ke ƴar aljanna ce. Annabin Rahama yasan da zuwanki" Yayi mata adda'a sosai. Sai yaran gida kowa yayi mata, sai su Baba Asshi da jiki yayi tiɓis tsoron Allah da nadamar abubuwan da suka faru ya shigesu. Cikinsu babu wacce batai nadama ba, domin babu wacce bata cutar da Baba Fhatsima ba. Banda zarginta da asiri da suke yi. Yaya Tasi'u da Yaya Jamilu ne suka fito da gawar Malam na biye dasu sauran yaran suka mara musu baya. Nan gidan ya kaure da salati da kuka har aka fita da gawarta. Duk wanda zaiyi magana a kanta halinta nagari yake faɗa, duk wanda zaiyi magana zai ambaci mai yawan kyauta. Gardawa ma sun ci kuka domin uwarsu ce. Tsabar al'ummar da Baba Fhatsima ta haɗa sai a ƙafa aka tafi da'ita zuwa makwancinta, gidanta na gaskiya. Daga haka jikin Malam ya rincaɓe dole akayi asibiti dashi cikin wani mummunan yanayi malam ya shiga, yanayin da dole a cire rai da tashin shi. Yaya Tasi'u da Amaryar Malam ne a asibitin. Su Yaya Jamilu da Baba Asshi suka ci gaba da karɓar gaisuwa. Ga Hadiza a kwance inda take ma bata sani ba. Abba da Toye suna wajen Shafa. Baba Asshi ce ta yafito Shafa ta zo inda take. "Shafa maza kije ki haɗa kayan karyawa aba Gwadabe ya kai musu asibiti. Matar wanku tana can bata ci komai ba. Ki haɗa akaima wan naku ma nasu. Kuje da Zaliha maza" "To Baba" suka tafi da Zaliha ruwan tea suka dafa, sai suka yi tuwon shinkafa dama Shafa na da lafiyayyar miyar kuɓewarta mai kyau tasha naman rago da bushasshen kifi. Fitowa su ka yi da kayan Abincin. Zaliha taje ta kirawo ma Shafa Gwadabe yazo. "Ga kayan abinci. Wannan Yaya za'a kaima. Wannan su Yaya Tasi'u za'a kaima. Yayan ta sauka ne?" "E ta sauka tun jiya da daddare ta samu mace. Nayi waya da su Bara'u da Tamu tun cikin dare asussuba suka kamo hanya. Ance su Babala da Yaya Hambali ma suna hanyar zuwa baki ɗaya. Shafa tace. "To Allah ya kawo su lafiya" Abincin ta bashi, ta koma cikin gida akaci gaba da amsar gaisuwa. Baba Asshi dawowa tayi ɗakin Baba Fhatsima da zama tare da su Ine. Dan duk wanda yazo gaisuwar ɗakin yake nufa. Surukan gidan aka wakilta ɗaura abinci a can gidansu. Domin baƙi daga nesa da zasu zo. Amman maraɗi garine na karamci in anyi mutuwa fanteka_fanteka ake shigo da abinci har sai anyi bakwai. GWADABE Ya isa asibitin farkawar Hadiza kenan, tana kukan cikinta na mata ciwo" "Dole zai miki ciwo ɗinki akayi miki Hadiza kibi a hankali." Cewar Anti Badi'a. Suna cikin wannan maganar Gwadabe ya shigo shi da Mammada da abinci. "Hadiza sannu da jikin" Cewar Mammada kenan. Gwadabe ya karasa kusa da gadon ya dubeta cikin so yace. "Yaya jikin naki Hadizata, ya sabuwar Baby da muka samu? Wannan Baby ta bamu wahala sosai. Sannu Anti Badi'a ina kwana?" Ya ƙarashe maganar da gaishe da Anti Badi'a. "Lafiya lau Gwadabe. Mammada sannunku fa da haƙuri" "Yauwa Anti Badi'a. Sannu da kwanan asibiti.Ni zan leƙa Malam zan kai mishi abinci, ina zuwa dan ba jimawa zamu yi ba" Hadiza bata gane me suke nufi ba sam dake a cikin zafin ciwo take. Ma'aikatan jinyar aka kira suka sake mata allurar bacci ta sake komawa bacci. Huduba Gwadabe yayi ma jaririyar da sunan Babala. "Gata Anti Badi'a nayi mata huɗuba da sunan mahaifiyata Hauwa Ai mata alkunya da Mami. Ni zanje in duba malam daga can zamu wuce. Amman Shafa zata zo ta zauna dan lallai ana matuƙar buƙatarki a can gidan" Jaririyar ya miƙa mata ya zaro kuɗi wadatattu ya ajjiye mata ya nufi ward ɗin maza. Al'amarin jikin malam ya girmama ba'a buƙatar kowa ya shiga ɗakin ma da yake. Abun jawo numfashine a bakinshi, da wasu robobi da ma'aikatan aikin jinyane kaɗai zasu iya sanin menene ( Khadija maidoki ana magana) suke sagale a jikin malam. Kuma likitoci sun tabbatar musu malam ya shiga koma sai dai aita tayashi da adda'a domun ba lallai bane ya tashi. Amman aita mishi adda'a. Ba'a shiga ɗakin sai dai ka hangoshi ta taga yana kwance, lokaci guda Malam ya rame ya zuge saiya sake tsayi da haske sosai. Jikin su Gwadabe a sanyaye hankali kuma a tashe suka bar Asibitin tare da Amaryar Malam suka tawo gidan tana buƙatar zuwa gida ƴan uwanta sunata kiran wayarta duk sun cika ɗakinta bata nan. Zuwa yamma sakaliya sai gasu Babala da su Goggo Iyatu da Goshi, da Yaya Hambali, da Yaya Halima, sai Yaya Haula. Jim kaɗan da zuwansu sai ga su Bara'u suma sun iso. Abun mamaki a cikin taron mata Gwadabe ya kwashi su Bara'u suka je yima su Babala ta'aziyya. Babala ta yi maza ta fice a ɗakin ma baki ɗaya. Goggo Iyatu ce kaɗai ta amsa gaisuwarshi itama a wulaƙance. Yaya Hambali kuwa ko da Gwadabe ya miƙa mishi hannu bai karɓi hannun ba. Yaya Tasi'u dake kusa dashi yace. "Haba Alhaji Hambali menene yayi zafi haka shi ba wuta ba. Yanzu yaronnan ba zaku sarara mishi ya samu yaci gaba da zumunci daku ba, ina laifin wanda ya gaisheka ko da bare ne balle jininka?" Murmushi Gwadabe yayi yace. "Ai babu komai Yaya Tasi'u. Yaya Hambali kayi haƙuri in sha Allah bazan sake ba ma" Iyakar abinda Gwadabe yace kenan. Kunsan masu kuɗi da saurin hasala sai Yaya Hambali yace. "Mitsiyaci kar Allah yasa ka sake. Kai ni inka kuma nuna ka sanni ma bazan yafe maka ba. Ɗan iska wanne irin baƙin ciki da tashin hankali ne baka sa Babala a ciki ba. Sanadiyyar baƙin cikinka har hawan jini saida ya kama mana uwa. Ɓace ka bani waje" Bara'u ne ya ɗaga Gwadabe suka koma tabarma matasa irinsu, yayi jigum yama rasa ta cewa. Yana sha'awar yaga ya shiga cikin ƴan uwanshi ayi wasa ayi dariya tare.shin sai yaushe wannan lokacin zai zo ne? Shikenan shi bashi da damar da zai ko da gaishe da Babala ta amsa mishi, wannan rayuwa wannan tashin hankali da mi yai kamane? Hadiza Ba ita ta farka ba sai da yamma sakaliya ta buɗe idanunta, harta samu ta ɗan sha tea shima kaɗan. Tana cikin ciwo sosai. "Shafa bani yarinyar in ganta" Shafa ta matso da yarinyar Hadiza ta ganta harda murmusawa Allah sarki uwa ( na jinjinama duk wata uwa ta faɗin duniya) "Allah ya rayata da imani. Shafa Gwadabe fa?" Shafa tace. "Basu jima da fita ba. Su Ine da su Sadiya duk sun zazzo dubaki ma amman bacci kike yi sun jima kuma. Amman yanzu zan kira Gwadabe in sanar mishi da farkawar taki. Baki ga yadda ya damu ba" Tana kai aya ta ɗaga waya ta sanar ma da Gwadabe farkawar Hadiza. Ba da daɗewa ba sai gasu shi da su Bara'u. Nan sukai mata ya jiki da kuma barka. "Yaya Bara'u ashe kun ƙaraso, ina su Sakinan suke?" Bara'u yace da Shafa. "Mun karaso. Su Sakina suna gida." Basu suka bar asibitin ba har sai zuwa bayan Isha. Sun leƙa Malam ma, jikinshi ba yadda yake gaskiya yana jin jiki sosai, sai dai ka hangeshi ta taga. Tare da Hadiza Shafa ta kwana washe gari da sassafe Baba Asshi tasa Yaya Jamilu ya kawota asibiti, ance gara a sanar ma da Hadiza abinda ake ciki ba sai an dawo da'ita gida taga dandazon ƴan makoki ba. Ƙawayen Hadizan na wajen aikinsu duk sunje gidan, sanar dasu da'akayi cewar ita Hadiza bata san me ake ciki bane yasa suka kasa zuwa wajenta su dubata. Hadiza tana ganin Baba Asshi da Yaya Jamilu jikinta ya bata akwai matsala, sai dai ko kusa ranta bai kawo mata mutuwace ba. Baba Asshi ta amshi jinjirar a hannun Shafa. Hadiza dai taga duk an gaggaisa cikin giirma da arziki, har Yaya Jamilu na tambayar ko akwai abinda take buƙatane, da mamaki tace mishi a'a. "Hadiza inaso ki sani a rayuwa duk abinda Allah ya ƙaddara afkuwarshi babu makawa. Inaso ki saka aranki cewar dole wata rana duk daren daɗewa mu iyayenki saimun koma kushewa, ko kuma ku ku koma. Allah yana iya ikonshi akan jinjirin dake ciki a haifeshi babu rai. Hadiza kiy haƙuri Allah ya amshi ran mahaifiyarku jiya mace mai haƙuri da yakana, macen da tun a duniya mijinta ya mata sitam na shiga aljanna. A iyakar zamanmu da ita alkhairi taita nufarmu dashi mu muna binta da sharri. A yanzu na gane gaskiya tashin hankali da rarrabewar kai ta kau." Da sharar hawaye ta ƙarashe maganar. Hadiza kuwa babu abinda take yi sai kuka. Amman yadda da ƙaddara wajibine a wajen ko wanne musulmi. Dole haka ta ɗauki dangana. Ta kuma yi farin ciki a lokaci guda na sauyin da aka samu a cikin gidan. Sai dai kuma zukata suna cikin taraddadin halin da Malam yake ciki. Haka akaita zaman makoki har zuwa bakwai. A wannan zaman an yi meeting kusan sau huɗu na haɗin kai domin manyan gidan so suke su samar da sauyi sosai kafin samun lafiyar malam. Kowa ya shiga tattayinshi. Ta bangaren yara mazan su da suka ɓata su akaba wannan ɓangaren suka tusa matansu gaba da zazzafan gargaɗi, da barazanar rabuwa dasu indai suka ƙi a zauna lafiya. Har wannan lokacin su Babala sunanan. Amman daga Gwadaben har Shafa Babala bata amsa gaisuwarsu. Yaranma da Shafa tayi karambanin kwaso su ta kawo mata saita ɓige da yima Iyabo Allah ya'isa ganin Toye ya fama mata mikin da Iyabo ta ji mata rauni. Ranar da akayi sadakar ukun a ranar aka sallamo Hadiza ta dawo gida. nan aka shiga tururuwar shiga gaisheta, haɗe da ta'aziyya, da kuma yi mata ya jikin Malam duk ita kaɗai. Hadiza da ƙannenta mata da yarta Zarah suka haɗa kansu sukaci kuka, a ranar sai mutuwar ta dawo musu sabuwa fil. Musamman da dangin Baba Fhatsima suka shigo yi musu sallamar zasu koma sai kuma sunzo sadakar arba'in. Su Babala ma a ranar suka koma, su Sakina suma shirin tafiyar dai suke yi. Gwadabe yasa an tafi dasu Toye ya sanar dashi ya nemi Uwani ta rakashi ya kaima Iyabo yaran su ganta. Dan a kwanakinnan yana wasu irin munanan mafarkai akan Iyabo da bai gane ma hakan ba. Kafin goman safe gidaje biyun ya zama iyakar iyalan gidanne kawai a ciki. Hadiza tana kwance shiru Gwadabe ya shigo da sallama, ya nemi waje ya zauna idanunshi jawur. Dan yanzu Babala taci mutuncinshi ta zazzageshi harda dana sanin haihuwarshi ma saida tayi. Lamarin daya addabeshi, tsoro da fargabar makomar rayuwarshi ya ratsashi. "Sannu da shigowa" Hadiza ta faɗa a raunane. Dubanta yayi dole ya danne damuwarshi, ya matsa kusa da'ita dab ta yadda suke jin saukar numfashinsu yana sarƙewa. "Yauwa Yaya jikin, ya ƙarin haƙurinmu?" Kukane yazo mata yayi wub ya tallafeta ya rungume matarshi tsam yana jin wani bala'in sonta na ratsa duk rassan jikinshi. Haɓarshi ya ɗaura a tsakiyar kanta ya lumshe idanunshi. Munanan furucin Babala na mishi kaikawo a ƙwaƙwalwarshi. A lokaci guda zuchiyarshi ke buga wasu irin tamburan tashin hankali. Sun daɗe sosai a haka. Sallamar Shafa ce yasa Hadiza zamewa daga jikinshi, amman suna manne sosai da juna ta shigo. Ganinsu a irin wannan yanayin sai ya ɗan daburta Shafa. Dama ruwan tea da faten dankalin turawane ta kawo ma Hadiza ta samu taci, tunda ance abu me ruwa ruwa zata ci gudun kar tiyatarta ta samu matsala. A teburin dake gaban gadon ta ajjiye tiran ." "Ashe ka dawo, sannu da dawowa. Su Yaya Bara'un har sun tafi?'" A sanyaye take magana kuma sai satar kallon irin zaman da suka yi a manne take yi. "Yanzu na shigo nazo duba Hadiza ne dama yanzu zan shigo." "A'a kayi zamanka kayi jinyarta har Allah yasa ta warware. Kaga a halin yanzu a cikin damuwa sosai take, barinta ita kaɗai akwai hatsari ni na yafeka har na tsawon wata biyu. Kuma zan dinga yin girki harna wata biyunnan" Tana kai aya saita nufi hanyar ficewa abunta. Gwadabe kasa magana yayi dan mamaki. "Shafa" Hadiza ta kirayi sunanta tana daf da fita. Cak ta tsaya a inda take ta juyo suka haɗa idanu. "Nagode sosai Shafa Allah yaa saka da Alkhairi." Murmusawa tayi tace. "La Yaya babu komai. Wannan shine zaman taren. Ummi ma tana wajena kinsanta da rigima duk saita dameku" Fita tayi ta koma ɗakunta ta zauna a bakin gado, ta lumshe idanunta wasu hawaye masu ɗumi suka zubo mata. Ji take soyayyar Gwadabe kamar zata tarwatsa mata zuchiyarta. Amman ta jima da fahimtar hankalin Gwadabe, da soyayyarshi kacokam akan Hadiza yake. Sallamarshi taji. Tayi saurin goge idanta. Ƙur ya ƙura mata idanu harya zo ya zauna dab a kusa da'ita bai dena kallonta ba. Tausayinta sosai ya hudashi. Juyo da'ita yayi ya fisgeta da ƙarfi ya mannata a ƙirjinshi ya mayar da hannayenshi ya nannaɗeta. A tare suka sauke ajjiyar zuchiya. Wani kuka ta sake mai ƙaramin sauti ta kasa mallakar kanta. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI CE ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU (17) IYABO:. Salati nake yi a hankali ina shan yaji tare da karkaɗa ɗan yatsana. Kamar an tashi Yafendo ta taso ta'iso inda nake ta dafa mun kai. "Jabu haihuwar tazo kenan? Alhamdulillah bari inje maza in taso Unguwar zoma tazo ta kula dake" Tayi maza ta fita, bata jima da fita ba saiga Baɗɗo tare da Hama sun shigo. Ɗago idona da suka yi ja nayi nasa a cikin na Hama. Sai naga ranta fes tana tsaye a kaina tana murmushin dana kasa fassarashi. Sauke kaina nayi naci gaba da roƙon Allah akan ya saukeni lafiya yasa in haifi mutum ba wani abunba. Kafin Yafendo ta shigo ita da unguwar zomannan na gama jiƙewa da zufa sharkab. Da unguwar zomannan ta shigo sai tace. "Ni a ƙa'idata bana karɓar haihuwa da mutane a ɗakin. Dan haka duk ku fice ku barmu daga ni sai ita" Fita suka yi aka barmu mu kaɗai. "Sannu Jabu ki saka dauriya zaki sauka lafiya. In baki ji nishi ba kar kiyi, hakan ke galabaitar da mata da yawa. Nishin zai zo da kanshi sai kiyishi iya karfinki nan da nan zaki haihu" Ni da unguwar zoma mukaita fama haihuwa dai tazo da tangarɗa kafin wayewar gari na fa galabaita bana ko motsin kirki. "Kaɓoji aje a nemo mota a kai yarinyar mutane asibiti kar tazo ta mutu, ko abinda ke cikinta ya mutu. Ni tsawon shekaru Ashirin dana shafe ina unguwar zoma banma taɓa karɓar haihuwa irin wannan ba. Cikin yana sama bai faɗo ba, kuma naƙudar take yi" Kafin Yafendo ta fita ta dawo jini ya ɓallemun. Baddo da Hama ne a kaina, in Hama ta faki idon Baddo saita danna mun cikina da iya ƙarfinta ni dama ganinsu sosai ma banayi. A gurguje a acaɓa aka tafi dani asibiti ni ina tsakiya Yafendo na baya ta riƙeni tamau, su Baɗɗo na biye dani. Ya ilayi ranar naga duniya, naga azabar da ko maƙiyina bazan mishi fata ba. A haka aka sake tarairayoni aka sakani a cikin akori kura zuwa cikin Girei Duk motsin da motar tayi da wani shiga rami sai inji kamar hanjina zai zazzago dan azaba. Muna shiga asibitin aka bani gado ma'aikatan jinya biyu suka rufu a kaina. Can a waje anata yima su Yafendo faɗan damme zasu bari in galabaita haka. Ni dai awana biyu a asibitin da kaina na haifo kyawawan yara maza ƴan tagwaye. Dishi_dishi nake ganin yaran ga gashi lub a kansu, gasu kamar yaran turawa da yaran a zuchiyata naji dif duhu ya maye gurbin hasken da nake gan. Ban sake sanin inda nake ba sai washe gari da safe na buɗe idona naga ƙarin jini a hannuna, ga jariraina a gefena, yara tsabar kyau kamar na aro. Juyowa nayi na ɗaga kaina na dubi Baɗɗo, na dubi Kari. Na lumshe idanuna inajin tsantsar farin ciki da Allah ya ƙadartama wannan yara zuwa Duniya yaran da kusan asibitoci sama da huɗu suka duba basu gansu a cikina ba. Allah yayi ikonshi gasu sun fito duniya. Inama Yaya Hamma yananan yaga kyawwawan abokananshi masu tayashi kiwon Shanu. Murmusawa nayi a lokaci guda wasu zafafan hawaye suka zubomun. Na farin cikine kukan na tsallake siraɗi. Murmushin kuma na taya Yaya Hamma farin cikine burinshi ya cika ni dashi mun haɗe mun zama abu guda, jininshi ya tsaga ya fito ta jinina yaran kamar an tsaga kara da ubansu. "Adda sannu yaya jikin?" Cewar Baddo ta yo kaina. Murmushi nayi mats duk da jikina babu ƙwari amman zuchiyata fes take. Da sauƙi jiki Baɗɗo. Sannunku, an sanarma Dada kuwa?" Dariya Kari tayi tace. "Sannu Adda. Dada ta sani tun jiya. Yau kwananki ɗaya a asibiti" Wata yinwace ta murɗa mun cikina da nake jin yanai mini ciwo_ciwo. Baɗɗo yinwa nake ji sosai" Da sauri Baɗɗo ta ɗauki kofi ta cikomun da kokko mai zafi. Kari ta taimaka mun na zauna, na jingina bayana da kan gadon. Ina shan kunun ina kallon yarana da aka lulluɓesu a cikin tawul ɗaya . Ma'aikaciyar jinyace ta shigo ward din tana bi gado_gado har ta iso gadonmu ɗakin duk masu jegone a kwance da jirajiransu abun sha'awa. Jinin da ake ƙaramin ta cire mun dama ya ƙare yanzu. Ta dudduba yaran dai haka, nima ta tambayeni ko akwai abinda ke damuna nace da'ita babu. Sai tace dani. Zuwa da rana zasu sallamemu ni da tagwaye muna cikin ƙoshin lafiya. Ta ɗauki yaran taita yabon kyansu dai haka ta ajjiyesu ta matsa gado na gaba. Yaran na ɗauka na ɗaurasu akan cinyata ina kallonsu da kyau. Wasu siraran hawayene suka gangaro a kumatuna. Ni da kaina nayi musu kiran sallah a kunnensu. Na dinga musu adda'a ina tofesu dashi. Ina cikin haka sai ga Hama, Safiya, Daso sun shigo da kwanukan abinci niƙi_niƙi. Ko ranar da da aka kaini gidan Hamma a matsayin kishiyar Hama, banga ɓacin rai makamancin wanda take ciki yanzu ba a fuskarta. Dani da yaranma sai naga tana wani harararmu, idanunta sunyi ja kamar ma tayi kuka. Safiya da Daso duk sukaimun ya jiki tare da yi mun barka. Wallahi babu abinda Hama tace dani. Anata kururuta kyan ƴan biyu tare da mamakin girma da kamanninsu da mahaifinsu. Funfurumfus Hama tayi ta zizarama idanunta kwalli taba banza ajiyarmu. Murmushi nayi cikin ƙarfin hali nace. Baɗɗo miƙama Hama yaran ta gansu" "A_a bassu bakya ganin nima ji nake yi da kaina." Murmushi nayi dama nasan ba ɗauka zata yi ba. Na gwadata ne kawai. Baɗɗo jakar hannuna an tawomun da'ita kuwa? Inason in kira Uwanine, da Debisi in sanar musu" Jakar Baɗɗo ta miƙo mun daman. Na ciro wayata na kunna. Burodami Debisi na soma kira na sanar dashi haihuwar. Sannan na kira Uwani itama na sanar mata. "Ai kuwa gara da kika sanar mun dan yanzu haka muna hanyar Adamawa tare da Bara'u abokin Gwadabe mijin Sakina" Sai naji gabana ya tattake ya faɗi da jin sunan Bara'u. Uwani ince dai lafiya dai ko?" Na tambaya a raunace. Hama idanunta ƙam a kaina tana karantata. "Lafiya lau sai alkhairi ke dai sai mun karaso kawai" Mu kai sallama na sauke wayata. "Jabu ga fa abinci Hama ta dafo miki. Baɗɗo ki zuba mata ko?" Cewar Daso kenan. Jin haka yasa nace. A'a ta bar abincin bakina babu daɗi sam. Baɗɗo in kina jin yinwa zaki iya ci, ni kam ko zanci sai anjima. Na koma nayi kwanciyata yarana suna kan cinyata ina jiyo ɗumin abuna. Miƙewa Hama tayi da fullanci tace. "To ni kam zan tafi gida, sai kun dawo" Tana faɗan haka ta kara gaba, Daso tabi bayanta. Safiya ce taimun sallama cikin mutunci. Suna fita Amaduyal yana shigowa da kwano a hannunshi. Farfesun kazar hausane Dada tayi tace a kawo mun. Nako ci da dama nasha romon sosai shima take bacci ya ɗebeni bani na farka ba sai wajajen azahar. Na farka ba da daɗewa ba aka kawo mana takaddar sallama da kuɗin da zamu biya. Baɗɗo ce taje biya dan Yafendo ta bata kuɗi daman ko za'a buƙata. Ina zaune jigum saina hango Bara'u a gaba rike da Taiyo da kahinde, Tabalbalin na biye dasu ga Toye a gefenta. Idanu na lumshe, Allahu Akbar naji daɗin ganin yarana fiye da tunanin masu karatu. Jina nayi kamar an tsundumani tsuungum a Aljanna. "Tsuntsun soyayya ƴan biyun aka sake haifo mana? Masha Allah" Miƙa mishi ɗaya nayi, Uwani ma ta amshi ɗaya. Sakkowa nayi na rungume su Toye dukkansu. Wato akwai ciwo rabuwa da yara, Toye ne kaɗai ya ganeni, su dai su Kahinde sunyi lub a jikina kawai. Naji daɗin ganinsu a cikin shiga mai kyau, da dukkan halamu Gwadabe ya samu rufin asari ba kamar yadda na sanshi ba. "Iyabo ashe Allah yayi yara sun fito duniya? Kai masha Allah ji yara tubarkalla kamarsu sak da ubansu." Ɗan murmushi nayi ma Uwani tana fama da ƙaton ciki hancinta duk ya buɗe. Bara'u barka da zuwa, yaya bayan rabuwa, yasu Sakina?" Dariya yayi yana jinjina kanshi. "Duk suna lafiya Iyabo. Da fatan kin samu kai lafiya. Banga maigidanba ko a waje." Ɗan murmushi nayi nace. Sun tafi cirani kiwo kamar yadda akasan fulani da fita kiwo." Murmusawa yayi yace. "Allah ya dawo dashi lafiya. Yara kuma Allah ya rayasu cikin aminci. Ga yara Gwadabe ya aikoni dasu tun daga Maraɗi yace a kawosu su yi wata guda, sai in dawo in ɗaukesu da yardar Allah." A Maraɗi kuma Gwadaben ya koma da zama?" Na tambaya da mamaki. " E Maraɗi yake da zama kusan shekara bakwai kenan. Gidan Baba Magaji wansu Babala. To yana auren Hadiza yarinyar Baba Magaji. Da Shafa ƙanwar Abokinmu Tamu, yaranshi huɗu ciki harda takwararki." Mamakine ya kamani. Gwadabe da mata biyu? Iko sai Allah, dama yana da ra'ayin mata biyu kena, ko bayan rabuwarmu ne ya samu ra'ayin? Kafin in gama tantance fari da baƙi Bara'u ya miƙo mun hoton diyar Gwadabe takwarata. Nasa hannu na amsa na zuba mata idanu kyakkyawa fara da'ita. Nayi farin ciki da Gwadabe yasa sunana ashe dai bai mance dani ba. "Kin ganta wannan itace Iyabo. Shafa kanwarmu itace ta haifeta, shine yasa aka kaita gidan ɗaukar hoto aka ɗauketa dan a kawo miki ki ganta." Allahu Akbar. Naji daɗi sosai Bara'u Allah yabar zumunci" Baɗɗo ce ta dawo daga biyan kudi. An gama komai sai tafiya. Sallama nayi da matan ɗakin muka wuce. Tare duk muka rankaya zuwa gida. Baɗɗo nasa ta kai Bara'u gidan Dada, ni kuma aka wuce dani gida. Wajajen bayan Isha can, bayan nayi wanka naci tuwo, Amaduyal yazo ya ɗauki abincin Bara'u da nasa akayi mishi, Da tsaraba Amaduyal yazo yace Bara'u ne yace a kawo mun. Su Toye suna ɗakin Yafendo ta janyesu. "Iyabo na ƙosa ki bani labarin bayan rabuwa. Da ganin ɗakinki abubbuwa da dama sun faffaru. Naji kince Hamma ya tafi cirani. Meke faruwane, ga kishiyarki naga sai dukan yaranta take yi tana baloƙoƙo?" Hmmm Tabalbalin meye ma bai faru ba?" Nan na shiga mata labari daki_daki harna dire mata. "Iko sai Allah Iyabo. Kina ganin rayuwa kekam iri_iri. Amman watarana fa duk sai labari, amman da kikayi gobara da saiki sanar mini kema kinsan zan turo miki da duk abinda kike buƙata, kuma zanzo ki ganni kiji daɗi. Baki ga yadda kika fita hayyacinki ba. Bara'u ma sai kallonki yake yi yaga duk kin lalace kin koma baƙauya fitik, jibi wata atamfa ruwan kwara_kwara a jikinki" Banso inyi dariya ba amman ni da Uwani muka tuntsure da dariya. Sallamar Yafendo Jabu, da Dadane ya katse mana hirarmu. Maraba Yafendona, Dada sannu da zuwa" Tabarma na shinfiɗa musu a gefe suka zauna muka gaggaisa, Uwani ta miƙo musu yaran. Sai ga Yafendo dasu Toye da Baɗɗo sun shigo. "Kunzo ganin mazajen naku kun kasa haƙuri sai gobe. Dada inyalli jam?" Dada ta yi ma Yafendo murmushi aka gaggaisa, suka ga su Toye tare da shi musu albarka. "Jabu wannan biyun naki macen naga sai ƙananun kuka take ɗanyi dai, tana ambaton Mama." Da yarbanci na kirata abun mamaki sai gata tazo na ɗaurata a cinyata nace. Menene kike kuka Taiwo?" Sai take ce mini ita gida zata tafi wajen Babanta. Nan dai Yafendo tai mata dabarar ta bari sai gobe sai a kaisu. Su Dada dai su kai mana sallama suka fita. Ƴan biyu sai sheƙa baccinsu suke yi, ruwan nonona inaji yana zuwa. "Iyabo ni ɗinnan fa a cikin damuwa nake sosai. Ni da ba dan wannan cikin ba, da kuma ina tunanin wahalar da yarana zasu sha a hannun matar ubansu ba. Ke da auren zan ajjiye wallahi in huta, na gaji matsaltsalu iri da kala. Ko kinsan yanzu ni da Hafizu sai gani sai hange baya iya yin mu'amalar Aure dani abun baya yiwuwa. Tun yana so, harya haƙura. To daga baya ma aka dena lissafin wani rabon kwana, sai sanda yaga dama yake shigomun. Dama kuma na daɗe da korarshi a aiki, amman ya samu wani Alhaji ya sai mishi victira yana lodin ƙauyuka. To akan matarshi ya tare, ni dai da yarana sai dai fa in ciyar damu. Ɗan sauƙin dana samu ma kasuwancin Allah ya dafa mun mun haɗe shagunan ma duka biyu na zuba kaya sosai, na ɗauki su Ummi aiki tunda su zuchiyarsu ta mutu" Ajjiyar zuchiya na sauke nayi ƙuri ina kallon uwani harta dire maganarta. Rayuwarnnan bata tafiya face da tarin tulin matsaloli sune abokan tafiyar rayuwar. Ke ina ke ina wani barin gidan aure kina da gidanki, kina da sana'arki? "A'a ni ƙuncine bazanta ƙunshewa ba Iyabo. Ke kinsan bani da daɗi. Rannan anyi haihuwa a salam layinmu. To mai haihuwar ƙawartace, ni kuma yarinyar kostomatace dan nina haɗa mata kayan haihuwa. Kinsan yarinyarnan saina shiga na taddata tana ba ƙawayenta labarin ai tayi asiri ta kashe na Hafizu gaba a gidana bashi da fus. Kaza_wa_kaza dai ni kuma sai gani. Zagewa nayi na kirɓata wallahi, a daren kwana muka yi ni da Hafizu muna rikici. Ke nifa bazan mutu Lokacin mutuwar tawa batai ba." A lokacin dai sai haƙura da hirar muka yi, muka kwanta. Washe gari da safe muka ɗaura. Ina zaune fitowata daga wanka ban daɗe ba kenan. Yafendo Jabu ta gama ma yara wanka ta muƙo mun su, na zura musu nono suka hau sha. Baɗɗo ta shigo da tuwo a kwano yaji yajin daddawa da manshanu sharɓan. Baɗɗo an kaima Bara'u abun karin da Uwani tayi mishi?" "Ai gashi nan ma a tsakar gida fitowarshi daga wajen yafendo kenan. Yace in kiraki ke da Adda Uwani shi zai koma" Yafendona tace. "Jeki maza. Baddo ke kuma ki fitar da ruwan wankan da kayan yaran ki wanke. Ni sai in zauna da yaran" Ajjiyesu nayi duk sunyi baccima, na saka takalmi da mayafi muka fito. Bara'u wai harka fito sai tafiya?" Taiwo na maƙale dashi gam. "Wallahi ai naso asussuba ma in koma gaskiya. Iyabo Allah ya raya, ni zan koma sai nan da sati huɗu zan dawo ɗaukarsu. Ga Taiwo ta ɗaneni so take ta bini fa" Kuɗi ya zaro nera dubu huɗu ya miƙo mun. Uwanice tasa hannu ta karɓa. Muka haɗa idanu da Hama wacce ta kafa ta tsare tana kallonmu "A siyi sabulu ayi wanki. Ni zan koma. Allah bashi in mai gidan ya dawo a gaisheshi" Godiya mai tarin yawa nayi mishi, na bashi manshanu soyayya da nono kindirmo cikin jarka, harda zakara nasa Baɗɗo ta kama aka ɗaure mishi. Nace ya kaima sakina. Godiya yayi ya fice, da ƙyar ya ɓanɓare Taiwo a jikinshi. Yarinyarnan tafi awa tana kukan banza harda birgima. Ina jiyo Hama na zage_zage a tsakar gida. Yafendona ce tai ta rarrashinta fa da ƙyar tayi shiru. Can maƙota suka shiga tururuwar zuwa, tare da dangi na kusa gida ya cika tab da ƴan barka. Kunsan ƴan biyu akwai farin jinine. Haka aka dinga zuwa ganin ƴan biyu. Kab zuriyar su Dada babu wanda yake da ƴan biyu sai nice na kafa wannan tarihin. Irin baƙin cikin da Hama ta dinga nunawa abun ba'a cewa komai. A cikin ruwan wankan jariran tasan yadda tayi ta jefa allurai biyu, Yafendona tana sa Hassan allurar ta caki duwawunshi wajen ya fashe sai jini. Dani da duk masoyana hankalin kowa ya tashi. Nifa tsabaragen ruɗewa fisge yaron daga hannun Yafendona nayi na shiga karanto mishi duk adda'ar da tazo bakina. Matan gida suka cika a ƙofar ɗakin kukan yaro har maƙota wallahi. Ana zubar da ruwan wanka saiga allura guda biyu. A masai Baɗɗo ta jefa alluran. Anata mana Allah ya kyauta, amman fa alkinkimar ko a tsakar gidanma bata. Sai sabon ruwan wanka Uwani ta ɗaura tayi zamanta har ruwan yayi zafi ta juyo ta kaawo ma Yafendona. Kafin magriba ba sai jikin yaro ya saki ba, ga zazzaɓi ya rabkeshi. "Iyabo ina zuwa. Bari kiga in koya ma matarnan hankali" Da sauri najawo Tabalbalin nace. Kul cikine da'ita kar a yi ta Hajiyayye da Yaya Uwa ( NA FAƊO DAGA BENE.. NA ZARCE RIJIYA) Batta a niya bi a niya. Na tofesu da adda'a babu komai. Yaran da ko duniyar ba'aso suka zo ba. Da Allah dai na haɗata har suka fito duniyar. Yanzunma na haɗata da Allah. Ammam in wani abun ya samu ɗana, ko kuma ya mutu baki ɗaya. Zanyi abinda ni da Hama sai dai mu yi mutuwar kasko" Dawowa Uwani tayi ta zauna. Ni dai ina riƙe da ɗa ko nono yaƙi kamawa. Abu fa kamar wasa bamu runtsaba a gidannan sai jefin asuba dana tuno bari in mishi karatun Qur'ani a kunne. na soma karanta mishi wallahi sai yaro ya sauke ajjiyar zuchiya, a_a ba sai bacci ba. Sannan ne hankalinmu ya kwanta. Ni dai dana soma baccin wahala saida na kai hantsi. A hakanma Cubu ce ta tasheni sunzo da yaran Baffa Musa. Yafendona tace. "Ai gara ki daure kije kiyi wanka. Me jego bata zama da yinwa a jikinta. Wankan na daure naje nayo, abincinma tutturawa nayi babu dai daɗi. Har dai zuwa rana yaran suna lafiya ƙalau babu wata matsala. Baɗɗo da Cubu ne suka goya biyu aka kaima Dada su ta gansu dan ba zata iya zuwa ganinsu ba a kunya irinta fulani. Dawowarsune Baɗɗo take faɗamun wai taga mahaifinsu a wajen Dada yana rarrashinta ta koma. Kafin in bata amsa sai ga sallamar gungun ƙawayen Hama sun shigo, harda ita da tun a tsakar gida da muka haɗu ban sake ganinta ba sai yanzu. Uwani ta miƙa musu yaran suka amsa. Wata zabiya a cikinsu tace. "Ba shakka yara sak ubansu, Amarya daga zuwa taci gida" Ta faɗa tana dariya kamar ba magana ta cusa mana ba. Uwani ta kalleta tace. "Taci gida, taci miji ba. Saima kunga ta sake haifo wasu ƴan biyun ko ƴan uku du maza tukunna. Marasa mutunci fitsararru zaku zo har ɗaki kuna watsar mana da magana." Ƙwace yaran daga hannunsu tayi tace. "Ku tashi ku fice mana da gani tatattun marasa tsoron Allah. Ke kuma Hama na dawo kanki da ba dan kina da ciki ba da saina miki ɗan banzan duka kafin in koma garinmu, Jabu ƙyaleki take yi kinsan karonmu ai babu daɗi" Hama ta taɓe bakinta ta miƙe tsaye da ciki. Ƙawayenta suka tashi tsaye suma. "Jabu kina ji ƙawarki na cin zarafin mutane kin kasa dakatar da'ita? Nifa ban gane me kuke nufi ba kuna dai son ƙalamun sharrine ni bani na saka allura a ruwan wankan yara ba. Kamar yadda kuma Jabu ta haifi maza ai nima abinda ke cikina kenan. Hamma kuma nawane kowa ya sani. Uwani ki bar ganin a baya kinci galaba a kaina ki rikeshi ya zame miki makani. A yanzu nafi ƙarfinki. Hafsatu mu fitar mata a ɗaki" Ni dai da uwar harara kawai nabi bayanta naja dogon tsaki nace. Jahilar mace wacce bata san kanta ba" Harta fita suka juyo a tare ita da ƙawayenta. "Ni kike kira da jahila? Oho dai da jahilcin nawa muka haɗa miji, mijin da yai miki gata harda uwarki da ƙannenki tunda shike ciyar dasu abun kunya" Da sauri na miƙe tsaye na nufi Hama ni da Baɗɗo. "Yayi kyau Hama sannunku da naimam fitina, ke dai kin kasa kwantar da kanki ku zauna lafiya ke da abokiyar zamanki, yanzu abun ya kai har Addan tawa kike zagi. Dan Hamma ya ciyar da'ita shine abun gori shi da yar mahaifiyarshi. Kul kika sake yinƙurin zagin Jabu a gidannan dan in ranki yayi dubu sai ya ɓaci wallahi." Yafendo ta ƙare mata tanadi tas, dalilin da yasa na koma ciki kenan. Ammam na ƙudure a raina na daina ragama Hama kwata_kwata a gidannan, in dai ta cakaleni zan mayar mata kamar yadda mudubi yake maida hoton fuska. A cikin zaman bakwai ɗinnan ba fa ƙaramin rikici aka dingayi da Hama ba tata ɓurza babu wacce ba'aiba. Komai masifa ta takurama su Taiwo sosai ni fa sai gidan Cubu aka kai yaran dan tsabaragen fitinar Hama. Ana jibi suna Uwani da Baɗɗo suka shiga kasuwa ranar kasuwa suka siyomun wasu kujeru marasa hannu dogaye biyu da wan_wan biyu, sai gadon katako waya goma sha biyu, da katifarshi. Uwani ta sai mun labule da ɗan abubuwan da baza'a rasa ba. Harda atampa kala biyu, sarƙa da ɗan kunne da takalmi daman uwani ta tawo mun dasu, da tulin kayan jarirai masu kyau. Dan ranar dasu Baɗɗo suka wanke kayan saida ya cika igiyoyin gidan kab. Ba Hama kaɗai ba fa har daga maƙota zuwa kallon kayan akeyi, dan basu taɓa ganin kayan jarirai masu yawan haka ba a cewarsu. Hama kuwa yi tayi kamar ta haɗiye zuchiya ta mutu. Ko yau ma hakance ta faru da rana fatse_fatse Hama na zaune tana ma yaranta tsifa ta saki wuyan riga nono duƙui a waje, ni kuma na fito shanyar kayan ƴan biyu da Cubu ta gama wankewa dan itama ba daɗi take jiba. Sai ga su Uwani suna dambe da kujeru. Bafa wasu kujeru masu kyau bane irinna ɗakinta ne amman wallahi sai kawai Hama ta fashe da kuka da kururuwa tayi ɗaki a guje. Dariya muka kwashe dashi ni da Uwani kawai. "Marar mutunci ni da nice kishiyarki tsirara zaki fice sabida duka, ƴar baƙin ciki, yara dai gasu Allah ya nufa sun zo duniyar, haka da zaran Hamma ya dawo zai sake ɗirka mata wani cikin ƴan biyun. Cikin awa guda ɗakin me jego ya fito fes, har sabuwar leda suka siyomun komai yayi shar dashi, atampopim kuma aka kai mun ɗinkinsu maƙotanmu. Washe gari Baɗɗo ta daddage ta yarfamun kitsona kaina ya fito shar dashi, su Dada da su Yafendo suma sai tasu hidimar suke yi. Da yamma saiga mijin Baɗɗo da raguna maza tiƙa_tiƙa biyu ya shigo. Baɗɗo dama tun bayan gama mun kitso ta tafi Girai ta siyo kayan miya da duk abun buƙata, shinkafa na bata kudi ta siyo mai kyau harda soɓo da kayan haɗinshi jallof muke so muyi da soɓo aci a more. Da yamma sakaliya sai ga Amaduyal tafe da Anty Mulka, da Iyaa Beji, da Bose. Da kayansu na gara rigi_rigi abun sha'awa." Mrs Bukhari ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU...... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 18 IYABO:. Harda lemun kwalba kiret biyar suka tawo dashi da gararsu riƙi_riƙi. Buhun shinkfa, garin Amala, wake, doya, manja, harda soyayyar jar miya aka tawo mun da'ita. Ga suturu ɗinkakku da aka kawomun Burodami Debisi ne yasa duk aka ɗinkamun kayan tas, ga takalmi ƙafa biyu ga su ɗankunne da sarƙa, ƴan biyu ma sun sha kaya, ni dai dana gansu naga kayan da suka kawo sai kuka kawai Anty mulka tace. "Ki dena kuka Iyabo wannan shine zumuncin ai. Kinganmu har anko muka yi wanda zamu saka ranar suna. Sai dai kin rame kin mugun lalace sai kace ba ke ba, wani abun akeyi miki a gidan. Ko kuma matsalar miji, ko kishiyane?" A jejjere tai mun tambayoyin duk sun kafeni da idanu suna son jin amsar bakina. Sai Bose tace. "Dole fa kiga ta lalace a ruga fa take aure. Jibi a irin gida da ɗakin da take rayuwa, kuma ita ta zaɓarma kanta zaman" Hararar dana doka mata ne yasa tayi shiru. Babu komai Anty Mulka nayi ciwo a cikinnan. Laulayin da ban taɓa yin irinshi ba nayi. Amman lafiya lau nake zaune da mijina, kishiya ita kuma zaman haƙuri akeyi da juna" Su Taiwo da Kahinde ne suka shigo da gudu da yaran Kari. Iyaa Baji tace. "Waɗanda ba yaranki na wajen tsuntsun soyayya bane? Harma yasan a inda kike aure kenan? Ahhh Ahhh Iyabo" Uwani ce ta ƙwaceni ta hanyar mu su bayanin yadda akayi, shine suka barni na sarara. Babu laifi sun samu tarba mai kyau daga wajen Yafendo, Dada ma ta ƙuƙuta tayo musu farfesun kaza an aiko musu dashi. Maƙota sai zuwa gaishe da baƙi suke yi, anata zuwa gulmar irin kayan da suka tawo dashi. Hama ma ta shigo tako daɗe sosai a ɗakin tafi awa saida ta gama ƙarema kayan da suka tawo dashi kallo tas kafin tai musu sallama ta nufi madafi kuma. Washegari ranar suna yara suka ci sunansu da suke zuwa dashi Hassan da Usaini. Tun asussubar fari su Anty Mulka suka shiga hura murhu aka ɗaura tukwanen girkin suna. Maƙota suka cika gidan dam jama'ar su Baɗɗo da Dada, da jama'ar shi Yaya Hamma. Dan kab matan abokanshi saida suka shigo taya aiki. Ta ɓangaren mazan gidan suna daga gefe anata aikin fiɗar ragunan suna, Uwani tana bakin rijiya ita da Bose suna gyaran kayan ciki. Ni kuma ina daga ɗaki ina saka kaya. Farin lace ɗin da Iyaa Debisi tayi mun shi na saka ɗinkin buba da zani na fito shar dani gashi nayi muguwar rama ta mamaki hatta mazaunaina da nake gadara dasu sun sace kaɗan ya ragemun. Sai nayi haske fuskata tayi fayau da'ita ga kitso nasha ga lalle na salateb an rangaɗamun. Ina sanya ma su Hassan kayan da Burodami Debisi ya siya musu yace a sanya musu suci suna. Sai ga Yafendo ta leƙo ɗakin Safiya na riƙe da ƙaton bahun shaƙe da kayan dangin maza, saida sukaimun turamen zani ashirin cib, ƴan biyu kuma sunsha rigina masu hangar roba da masu hangar ƙarfe, omo da mandula da nabkin Kam mun samu da wasu wando me kala kala na yaran fulani. Da wata riga mai ruwan hoda, bulu, yallo. Nasan kun ganeta duk uwar da tayi renon ɗa shekaru ashirin baya ta san wannan riga da wannan wandon. "Jabu ga namu kayannan babu yawa ayi haƙuri, yanayin garinne kinga anyi annobar Dabbobi an samu karayar arziki sosai" Murmushi nayi . A raina ina tuno haihuwa biyu da nayi a gidan Gwadabe, a leda ake kawomun kayan dangin miji shima a wulaƙance. Nagode sosai Yafendo mai yawan kenan ai. Dama yanzu nake son in gama a fitar da kayan da su Bose suka tawo dasu ma. "Ki barshi in Adda Daso ta kawo na wajenta sai a saka a bawo biyu a fito dashi a shimfiɗa tabarma haka muke yi. Tubarkalla kunyi kyau ke da yaran. Naga yayyensu ma suna tsakar gida duk anci kwalliya" Murmusawa kawai nayi ta saki labule ta koma ɓarayinta. Ina gyara ɗaurin ɗankwalina saiga Kari da Cubu da kaya niƙi_niƙi a buhu sun shigo dashi, daga ɓarayin Yafendona suke saida aka kai mata sannan tace a kawo mini. Uwani ce ta shigo. "Iyabo wannan man kamar bazai isa ai suyan kayan cikinnan ba gaskiya. Ahh cancaɗi kaga Amarya a gidan Hamma. Kai inama angon ƙarnin yananan zanso ganinshi a wannan rana" Dariya nayi dan ta sosa mun inda yake yi mini ƙaiƙayi. Tun a daren jiya nake kewar rashin mijina a tare dani a lokacin da nafi buƙatarshi. To kafinnan Uwani zo kiga abubuwan arziki da aketa samu. Sannan a sakasu a bawo a fitar tsakar gida kamar yadda suke yi a al'adance" Nan Uwani sukaita jejjera kaya, ta ɓangaren Dada ma masha Allah ƴan biyu sun samu kaya sosai. Bawo uku aka fitar shaƙe da kaya. Nan maƙwabta akaita tururuwar zuwa ganin kaya. Da bakinsu suke labarin tunda ake haihuwa a rugar babu mai jegon data kaini goshi. Hama kuwa kamar zata haɗiye zuchiya ta mutu ta huta da baƙin ciki. Jallof ɗin shikaface sai zoɓo da Amala da miyar ewedu da miyar tumatur da taji ganda. Dan tafi da gidanka su Iyaa Beji suka yi na bushasshiyar ganda, tun jiya da dadare aka jiƙata cikin bokiti da ruwan zafi. Maƙwabta akaita bi da abincin suna, gidan sunan cike da yara da manya, kowa ka gani abinci da lemun kwalba yake ci. Ina cikin matan abokan Yaya Hamma suna bani tasu gudunmawar, mai atampa, mai omo, mai kayan yara, masu miƙo kuɗi nayi sai ga Hama ta shigo babu ko sallama. Ganin na canja kaya nasa atampa me kyau dinkin ya zauna sosai a jikina saita sake ɓata ranta. "Danginane abincin da aka bani bai ishesu ba. Ga kula a zubo musu. Mutum biyu basu samu lemun kwalba ba sai zoɓo" Kular hannunta na karɓa na miƙa ma Uwani dake zuzzubama jama'a abinci. Babu musu ta cika mata kular tab da jalob ta ɗaura mata kayan ciki. "Gashi lemun kwalba ne ba zasu iya samu ba. Kinga waɗannan lemun kwalbar da masu shi, suyi haƙuri da zoɓon da suka samu ma" Cewar Uwani kenan. Hama dai ganin idanun abokan Hamma sai tace. "Ai babu komai Uwani. Hakanma mun gode" Ta karɓi kularta ta fita ɗaya daga cikin matan abokan Yaya Hamma sai kurantata take yi tana cewa tayi kyau wannan kwalliya haka. Haka dai wannan suna ya gabata sai yamma lis kowa ya watse, akabar ƴan gida da wanke_wanke. Tare duk aka haɗu akayi wanke_wanken ragowar abinci daya rage kuma matan gida duk suka ɗebe ko wacce tana faɗin ta huta da ɗaura tuwon dare. Sai bayan isha su Uwani suka kammala aikinsu tsab. Uwani ta shigo da banƙararrun ragunan da aka rataye a tsakar gida. Waɗannan ragunan fa Uwani" "So kike a bari a waje a sace? Uwargidanki tun magriba take sunturi a lungunnan kuma duk wucewa sai ta kalli ragunan taja ƙwafa na jima ina lura da'ita. Yanayinta kaɗai ya nuna ba mutuniyar arziki bace. Cewar Anty Mulka. Dariya nayi nace. Yanzu saita ɗauki rago to ta kaishi ina? Uwar harara Uwani ta doka mun, nayi mata dariya kawai. Washe gari duku_duku su Iyaa Beji suka tashi da suyar rago. Su Baɗɗo kuma sunata kiciniyar haɗa musu karim kumallo. Yafendona ce ta juyo ruwan wankan yara, nima ta kai mun nawa. "Maza Jabu je kiyi wankan kar ruwan ya huce" Mayafi na ɗauka na fito. A ƙofar bukkata na tarda Taiwo da Kahinde suna zaune suna kuka. Kallonsu nayi tausayinsu ya kamani, tsugunnawa nayi a kusa dasu. Na shiga rarrashinsu na samu su kai shiru nace su shiga ɗaki su kwanta a kan gado. Ai kuwa babu musu suka tashi suka shige. Murmusawa nayi nabi bayansu da idanu. Hawaye suka taru a idanuna. Wallahi barin yara a wani gidan babu daɗi. Kuma duk yadda mace takai sai yarannan sun mance da'ita kuma zasu kasance babu wannan shaƙuwar ta ƴaƴa ga mahaifiyarsu. A hakama Gwadabe yayi namijin ƙoƙari sosai da har ya aiko a kawo mun yaran. Da ƙyar naja ƙafata na shiga wankan, ban jima ba na fito, na samu Yafendona tana yima ƴan biyu rawa sunsha fararen ovaroll sunyi kyau yara kamar yaran Turawa. Kan gadona na kalla Taiwo da Kahinde sunyi baccinsu sai ajjiyar zuchiya suke saukewa. Haka aka soya namannan guda ɗaya surutum Yafendo tace a ciremun ɗayan ragon suka kasa kashi huɗu. Ɗaya nasu Yafendo da mutan gidan. ɗaya na Dada da ƙannena. Ɗaya na maƙota, sai ɗayan na dangin Babana. Yafendo tace in dibarma Hama a nawa, an kuma bata kai da ƙafan rago ɗaya, ɗayan da safe shi aka dafe mun naci. A leda na ƙulla mata na tura yara suka kai mata. Nayi tunanin ba zata karɓama ma sai kuma ta karɓa. Na ƙarama su Iyaa Beji a nawa da Uwani. Washegari su Iyaa Beji suka kama hanyar Kano. Uwani dama tace saita yi sati guda kafin ta koma. Wata ranar alhamis muna zaune a tsakar gida ni ina wanki, Uwani na yi mun kwalimar ɗakina saiga Hama ta fito da jaka niƙi_niƙi da yara wai gidansu zata koma ita acan zata haihu taci gaba da zama har sai Yaya Hamma ya dawo. Kai kawai Yafendo ta girgiza tace. "A sauka lafiya. Ni bazan hanaki zuwa gidaba tunda wanda kike zamanshi bayanan. Amman ki ajjiye yara a gidansu suci gaba da zama a cikin ƴan uwansu. Jabu ki karɓi yaranki kici gaba ds da riƙesu har zuwa sanda zata dawo." Bafa haka Hama taso ba. Cikin fishi ta ajjiye jakar yaran tayi ficewarta tana maganganu marasa daɗi. "Allah ya shirya. Jabu kici gaba da haƙuri nima kaina haƙurin nake yi da Hama. Tunda dai aka auroki gabaki ɗaya kafatanin halayenta suka sauya. Babu komai Yafendo. Ku kuma kuzo mu shiga ciki ko?" Na tattare yaran muka shiga cikin ɗakina dasu. Ana gobe Uwani zata tafi da daddare na tattaro mata kayana atampopi kusan kala goma cib nace duk ta ɗinka mun inna tawo sunanta sai in tawo dasu. "Ki haɗo da waɗannan rigunan masu zubin ƴan ƙauye dukka sai in shiga kasuwa a yi canjin kasuwa in zaɓa musu masu kyau, tunda naga kin samu dayawa" Ai kuwa kin kawo shawara me kyau." Tattaro mata nayi kusan duka kaɗan na rage. Washe gari sassafe ta yi mana sallama ta kama hanya, kafin dai ta tafi ta faɗamun watannin daya rage haihuwarta sabida kintata zanyi in tawo tunda bamu da network. Haka rayuwa taita tafiya su Taiwo sukaita bani wahala in wannan ya warke ciwo sai wannan ya kama, canjin ruwa da zaman ƙauye duk saiya sa suka rame ga ƙuraje caɓa_caɓa ya fito a jikinsu babu masaka tsinke. Ranar da suka cika wata guda a ranar Bara'u ya tawo ya kwana a gidan Dada washe gari suka wuce. Na haɗama yaran goma sha tara na arziki. Taiwo Atampa biyu na bata. Na kulle atampa biyu daban na matan Gwadabe. Toye da Kahinde nasa Uwani ta sai musu kaya kala bibbiyu ƴan kanti duk da dai irin na ƴan ƙauyene amman dai na siya musu. Na siya ms Iyabo kaya itama. Dada ta haɗa musu tsarabar ƙauye, hakama Yafendo, da su Baɗɗo. Aka dai haɗa musu tsaraba rigijib harda zabi huɗu aka haɗasu dashi wai suyi kiwo. Kuɗi masu yawa Bara'u ya miƙo mun da kaya cikin babbar ƙatuwar leda yace wai inji Gwadabe yace a bani kuma yanayi mun barka. Allah sarki Gwadabe. Dan Allah Bara'u kace nagode Allah ya saka mishi da Alkhairi " "Babu komai ai tsuntsun soyayya. Naso mu tawo da Sakina ma amman tayi nauyine sosai haihuwa ko yau ko gobe. Amman wata rana kwatsam zaki gammu." Allah sarki Sakina Allah ya raba lafiya. Nima indai na shigo kano nanda wata ɗaya in sha Allah zan shigo Takai ɗin da izinin Allah." Da haka mu kai sallama ya tusa yaran a gaba suka tafi. Mu kuma rayuwa taci gaba da garawa damu. Shayarwa tasa nayi kyau na ciccika sosai. Hankalina ya kwanta sosai a tafiyar Hama gida har ga Allah ni dai saida nayi fatan inama karta dawo. Gabaki ɗaya gidan da matan gidan duk sun sake. Ƴan biyu kuwa suna ganin gata a wajen Yafendo da ƙannen Yaya Hamma. Haka dai naci gaba da shayar dasu cikin tsabta da lafiya. Abun mamki nayi ƙiba sosai baku ganni ba, sabida ƴan biyu suna da tsotso sai nima cin abincina ya ninka, dani dasu duk mukai ɓul_ɓul damu." Yau tun safe na tashi da shirin zuwa dubo Dada. Da wuri naima yara wanka nayi mana wankin kayanmu na shanya, na goya ƴan biyu na fito. Ɓarayin Yafendo na nufa nai mata sallama inaso in je dubo Dada daga can zan leƙa Cubu dan ance bata ji daɗi ba." "Sai kun dawo ƙila anjima nima in leƙo gidan in duba Adda dan jiya ciwon kai ya sata a gaba" Ni banma sani ba sai yanzu da nake ji. Ayya ai kuwa zan tafi mata da ƙwayar bature ta haɗiya. Sai mun dawo Yafendo" Fitowa nayi duk inda na wuce sai na tsaya an gaisa sun ga ƴan biyu kafin in wuce. Ga rana sosai a garin zafi akeyi sosai safiyace amman har rana tayi zafi. Sai naji idona wannan marar ganin ya soma ciwo har yana zubar da ruwa. Da sallama na shiga gidan Dada ina haki abunka da masu kitse. A tsakar gida na samu Dada a kwance Yusufu na mata fifita Kari kuma tunda ban ganta a tsakar gidanba nasan bata nan an tafi talla. "Jabu kune da safe haka? Saifa da nace da Baɗɗo ba sai sun faɗa miki ba shine saida ta faɗa" Zama nayi a kan tabarmar, na sunto ƴan biyu da suketa kukan zafi. Yusufu ya karɓi ɗaya Dada ta tashi zaune itama ta miƙo hannu in sa mata daya. A_a Dada kiyi fama da kanki Usaini nauyine dashi ga tumbuɗi" Murmushi tayi tace. "Kema lokacin da nake koyonki ai kin fishi girma da nauyi. Cika bayana dam kike yi. Duk inda na wuce sai an kalleni, har ciwon ƙirji saida ya kamani a goyonki. Miƙo shi" Murmusawa nayi. Ni dai Allah ya jarabceni da tausayin Dada. Sanyin muryarta kaɗai ka iya cika idona da ruwan ƙwalla. Usaini na miƙa mata na tashi na ɗebo ruwa a randa na ɓalla mata fanadol biyu. Na bata ta sha ta kwanta. Na samu Yusufu ya riƙe mun yaran nayi mata kwalima, na wanke mata tufafinta tas na share tsakar gidan. Bani na bar gidan ba saida na yi mata miyar tumatur na aika Yusufu ya siyo mun nama da shinkafa. Sai wajajen biyun rana na nufi gidan Cubu. Da sallamata na shiga cikin gidan abun mamaki kishiyoyinta da girmansu wasu da yaransu a gidan miji ma amman suka saka Cubu a gaba uwargidan ta zauna a ƙaton cikinta sai ihu take yi. Ragowar kishiyoyin suna ranƙwashinta. Subhanallaah me zan gani kasheta zaku yi ko me?" A firgice suka juyo suka zuba mun idanu. Hawaye suka gangaro a kumatuna. Cubu numfashinta sai kokuwa suke yi ita dashi" Mrs Bukhari ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 19 GWADABE:. Ya daɗe yana shafa bayan Shafa amman ta kasa bama zuchiyarta haƙuri ta dangana. Zuchiyarta ta daɗe tana ƙunsan wannan takaicin na yadda yake kasa ɓoye soyayyar Hadiza a ko'inane ko kara baya yi mata. Sai dai ita tayi mishi kara ta tayashi son abinda yake so. Haka Hadiza ƙiri da muzu taƙi amincewa asa ma ɗiyarta sunan Iyabo. Amman ita tambaya ɗaya yayi mata ta amince mishi. Ko kusa bawai dan tana son sunan bane, tayi hakanne domin son abinda mijinta yake so. Duk kawaici na danginta saida saka sunan Iyabo ya taɓa ransu, Tamu ne yayi kinini a cikin lamarin ya hanasu tayar da zancan. "Kiyi haƙuri Shafa koma menene ya saki kukan na roƙeki kukanki yana dafani? Da sauri ta ɗago ta zuba idanunta a nashi a ƙoƙarinta nason ganin da gaske yake yi kukan nata na gasa ranshin kuma. Ja taga idanunshi sunyi harda maiƙon hawaye. A hankali ta sauke kanta a sanyaye tana sauke ajjiyar zuchiya. "Inason sanin damuwarki da abinda ya sakaki wannan kukan. Ko dai ganin Hadiza da kikayi a maƙale danine ya zaburo miki da kishin ki uhm?" Shiru tayi tana share hawaye. Niyyar tashi daga jikinshi tayi yayi wuf ya sake dawo da'ita jikinshi. Kyakkyawan riƙo yayi mata ya tallafo haɓarta tare da yima bakinta riƙon alewar yara. Wata duniya suka shilla ta masoya Gwadabe da Shafa sunma mance a duniyar da suke jin daɗin rayuwarsu kawai suke yi. Labulen ɗakin suka ji halamar kamar a ɗage yake. Shafa ce ta yi saurin juyowa suka haɗa idanu da Hadiza dake tsaye tana hucin kishi. Gwadabe na zaune ko gezau baiyi ba balle yayi yinƙurin tashi. "Lafiya zaki buɗemun labulen uwar ɗakina babu sallama balle neman izini, in da kinga abinda yafi haka kuma fa? Kinga hakan ai bai dace ba. Baban Abba tashi kuje Allah ya bamu alkhairi." "Ni kike faɗama wannan maganar, ashe ba har zuchiyarki kika sallamamun mijin ba? In ba haka ba daga zuwa yayi miki sallama zaku ɓige da soyayya ba kunya babu tsoron Allah. To yayi zamanshi anan wajenki ki bashi abinda yake buƙata. Namiji da kishiya duk amincinku watarana sai sun munafurceka" Tana kaiwa nan ta saki labulen tayi ficewarta. Shafa ta dubi Gwadabe da taga yayi shiru baice komai ba, shi bai tashi ba, shi bai magantuba. Haƙiƙa taji ciwon maganganun Hadiza, ko dai dama ba yau ta soma yi mata ire-irensu ba, dannewa kawai take yi da ƙoƙarin a zauna lafiya" "Shafa kiyi haƙuri ki daɗa zan kuma yima tubkar hanci danna fuskanci Hadiza zuma ce sai da wuta. Ni na ɗauka lallami zai bi da'ita ashe ba haka bane. Jeki shinfiɗe yara sai ki dawo" "Kaifa ai ya kamata kaje ka rarrashi ƴar gwal ɗin taka da baka ƙaunar ganin ɓacin ranta." Shafa ta faɗa cikin sigar kishi da muryar tausayi ainun. Kunya ta shigi Gwadabe dan tabbas yasan Shafa akwaita da kawaici da yakana. "Ke dai jeki ki dawo, anan zan kwanta ke ba a gabanki tace in yi zamana ki bani abinda nake buƙata ba?" Murmushi Shafa tayi kawai ta miƙe taje ta yima yara shinfiɗa ta dawo ta tarar har Gwadabe ya tuɓe yana kwance." "Baban Abba kayi haƙuri karka biyema tuburarriyar matarka in kayi la'akari da mutuwar da akayi mata da tiyatar da akayi mata. Inma kana son ɗaukar mataki a wannan karon na roƙeka ka daure. In dai Yaya ce halinta ne zata sake ai." Da ƙyar Shafa ta sha kan Gwadabe ya tashi ya mayar da kayanshi yai musu sallama ya fice. Hawayen baƙin ciki Shafa ta sake sharewa ta sake komawa wajen yaranta. Da salllama Gwadabe ya shiga ɗakin fuska a turɓune, Hadiza tana zaune amman ko kallo bai isheta ba balle har ta amsa sallamarshi. Abinda ya sake ƙular dashi kenan, amman sai ya rabu da'ita ya haura gado ya kwanta yana shafar fuskar jaririyar da sai mutsu_mutsun somin kuka take yi. Ai kuwa kamar jira jaririyar take uban ya taɓata ta ɓalle da kuka. Nan ta shiga canyara kukan inya_inya Hadiza tayi funfurunfus taƙi juyowa ma balle ta san yarinyar na kuka. Shiko Gwadabe mamakine yasa ya kasa cewa da'ita uffan sai idanu da yake bin Hadizar dashi. "Ke Hadiza wai baki ji yarinyarnan tana kuka bane koko Yaya?" Yayi maganar da kakkausar murya. Hadiza ta sake bama banza ajiyarsu lamarin daya fusata Gwadabe ƙarshen fusata, fusatar da bai taɓa yin irinta ba." "Wai shin ba dake nake magana bane Hadiza kina da hankali kuwa?" Wallahi Hadiza ta sake yin watsin ruwan tsarki da Gwadabe harma ta yi kwanciyarta a gefen gadon ta juya mishi baya. Miƙewa yayi da jaririyar ya shiga jijjigata dan baƙin ciki da ɓacin rai jikinshi har rawa yake yi, take kanshi ya soma sara mishi. Shi kam ya gaji da matsalolin Hadiza. A yau yayi ɗan daka ce bai auri Hadiza ba ya rabu da'ita ta auri wani kamar yadda malam yace mishi. Lallai Hadiza mahaukaciya ce sosai. Kukan jaririyar ya karaɗe kab gidan harda ma can cikin gidan. Auwala ne ya tawo shi da matarshi suka shiga bubbuga kofar Gwadabe. Kafin yazo ya buɗe Sabitu ma ya fito. "Ko lafiyar wannan jinjira wannan kuka ai yayi yawa Yaya Auwala" Cewar Sabitu. Dubanshi Auwala yayi tare da jin sanyi a ruhinshi jin ɗan uwan nashi gudan jininshi ya kirashi da Yaya. Allah sarki rayuwa. ( Da ace mata zasu gane rarrabe kawunan ƴaƴa ba abu bane me kyau, ba kuma hanyace mai ɓullewa ba da sun huta. Ƴan uba ba abokan gaba bane. Ƴan uba abokan junane dangin junane.) Gwadabe ne ya fito da jaririya a hannunshi tana shiɗewa. "Wai lafiya Gwadabe Hadizan bata gidanne yarinya take irin wannan kuka na fitar hayyaci" Auwala ya tambaya. "Tana ciki taƙi karɓar yarinyarne kawai. Idanunta biyu tana ji. Iskanci da wulaƙanci take ji" "Kaji aikin rashin hankali na Hadiza ko. Ku bani waje in shiga in ci ƙaniyarta wawuya kawai" Cewar Mammada daya ƙaraso wajen. Ya amshe yarinyar yanata jijjigata. Allah sarki shi gashi haihuwar suke nema idanu rufe Allah bai basu ba. Ita Hadiza ta samu tana shirme. "A'a Mammada banda duka kasan anyi mata tiyata abi komai dai a hankali." Cewar Auwala kenan. Auwala ya dubi Sabitu yace. "Kaje shiyyar su Yaya Tasi'u ka taso su zata gane kurenta." Da sauri Sabitu ya tafi aiken da Auwala yayi mishi. Gwadabe ya nufi ƙofar ɗakin Shafa da jaririyar ya shiga aikin buga ƙofar Shafa. Buɗe sakata tayi Gwadabe ya shiga da jaririya a hannu ya miƙa ma Shafa. Ba musu tasa hannu ta karɓi yarinyar. "Ki bata Mama tasha, ki barta a wajenki tunda uwar bata sonta" "To amman kafa..." "A'a ni ban sanki da musu ba Ina girmamaki akan hakan. Ki sani nasan abinda nake yi." Haɗiye maganar dake bakinta tayi ta koma kan kujera ta zaro Mama ta zura ma jaririyar a baki. Nan ta soma tsotso tana sauke ajjiyar zuchiya" "Allah yayi miki albarka Shafa nagode ƙwarai da wannan soyayyar. Matsayinki na musamman ne" Yasa kai ya fice. Shafa ta girgiza kanta tana mamakin hali irinna Hadiza. Fitowar Gwadabe daga ɗakin Shafa yayi daidai da isowar Yaya Tasi'u harda Anti Badi'a dake biye dasu. A falon Hadiza duk suka taru. Gwadabe ya basu labarin iyakar dalilin Hadiza na azabtar mishi da yarinya da tayi. "Wallahi Yaya Tasi'u haƙurina ya kusan ƙarewa akan sha'anin fitinar Hadiza. In taso in kai ƙarane bazan iyaba. Ni wannan matsalar sabuwace a cikin rayuwata. Ni wallahi tsohuwar matata kafin ince tayi take yi. Haka ma Shafa take yi mun. Amman fa Hadiza ita kullum a ƙoƙarin ganin laifina take duk iyakar kyautatawar da nake yi mata." Hadiza tana tsakankanin yayyenta kanta a ƙasa sai jijjiga kanta take yi da dukkan alamu dai maganganun bakin Gwadabe suna dukan ranta in akai la'akari da Iyabo da Shafa da shi Gwadabe ya ambata. Gyaran murya Yaya Tasi'u yayi yace. "Allah ya kyauta. Ni na ɗauka wani gagarumin abune ya shiga tsakaninku ma da wallahi bazan ko sakko daga gadona akan wannan shirmen ba ko Auwala ya isa yaba Hadiza kashi. Kaga Gwadabe kar ka bari ƴan uwantaka ko zumunci ya hanaka gyara gidanka. Kai kasan komai akan abinda yaita gudana a baya a cikin gidan Malam. Duk da muna fatan komai ya zama tarihi tunda ga Sabitu abun sha'awa a zaune a gabana a ɗakin Hadiza kuma. Ke kuma Hadiza ni zan fi so ki kashe aurenki ki kima cikin gida ki dinga kallon rayuwar tsohon mijinki da tsohuwar kishiyarki. Ku kuma ku tashi kowa yaje ya kwanta." Ai nan Hadiza ta ɗago kanta ta dubi Gwadabe duba na wulaƙanci, ta maida dubanta kan Yaya Tasi'u tace. "Wallahi Yaya Tasi'u Gwadabe ba adali bane. Yafi fifita Shafa da yaranta dan kawai tana da maza a...." "Tas tas Yaya Tasi'u ya mari hadiza. Auwala ya zuba mata ranƙwashi a tsakiyar kanta, Sabitu ya zubo mata harara. Mammada da Gwadabe ne suka kwaceta dan Auwala zagewa yayi yana neman dukanta sai da Anty Badi'a tayi saurin shiga tsakani. "A_a Baban Sailuba karfa kuyi kisan kai fa. Yarinyarnan ɗanyan jego take yi, aiki kuma akayi mata. Ke Hadiza tashi ki shiga ɗaki kinji. Gwadabe ka kawo mata jaririyar tata." Da gudu Hadiza ta shige ciki Sabitu ya bita da mangari Allah ya sota bai sameta ba. "Wawuya shashasha in baki yi sa'a ba gobe zan sa Zara ta daka mun ke a gidannan" Cewar Yaya Tasi'u kenan a tare suka fice Gwadabe kuma ya kulle ƙofa yayi kwanciyarshi a doguwar kujera yana tubka yana warwara. Cin mutuncin da Babala da Yaya Hambali suka yi mishi sai dawo mishi yake yi. Yana mamaki ainun ace uwa ta tsugunna ta haifi ɗa ta dena sonshi. Duk da Yaya Hambali shine kanwa uwar gami a tsakaninsu. Mafi yawa_yawan lokaci Yaya Hambali ke zuga Babala ya harzuƙata ta hasaka har ta dinga furta mishi kalaman da basu dace ba. Wayarshi ce ta shiga kuka ya zaro a ajjihu yaga Bara'u ne. "Kayi haƙuri ban kiraka naji kun sauka lafiya ba sai kaine ka ɓige da kirana. Ina fatan kun sauka lafiya?" Bara'u yace. "Lafiya lau ka gammu a tsakar gida ma da yaran du. Zuwa jibi sassafe zan kwashi yaran muje Kano gidan Uwanin. Inma bamu je wajen Iyabo a jibin ba tunda ba zaman kanta take yi ba. Zan bar yaran a wajenta in tasa mun lokaci sai inje mu je " Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke. "Allah ya nuna mana. Ina fatan ku sameta cikin aminci in sha Allah. Sannunku Allah ya bar zumunci a huta gajiya" Da haka suka yi sallama ya ajjiye wayarshi sai ga Hadiza firit ta fito tayi tsaye a kanshi tana jijjiga. "Burinka ka kaso auren tsohuwar matarka dai kai ka sake aure abinka. Ta dai tabbata Iyabo dai asiri tayi maka. Bata ƙarƙashin inuwar aurenka ma adda'ar aminci kake yi mata. Allah zai saka mana mugu azzalumin banza" A fusace Gwadabe yayo kanta gadan_gadan dan idanunshi sun rufe hannu yasa ya tureta ta faɗi. Da dukanta ma yaso yayi tausayinta yake ji ga tiyata a jikinta, ga rashi babba da akayi mata. "Wayyo Allah ka kasheni a kan tsohuwar makirar tsohuwar matarka." Da sauri Gwadabe ya juyo me zai gani Hadiza face_face a cikin jini tana riƙe da wajen da akai mata tiyata. Ranga_ranga suka nufi asibiti a motar Yaya Tasi'u. Tun daga gida Yaya Tasi'u yake faɗa har suka isa asibiti. Kuma Hadiza yake ma faɗa duk da a sume ma take. Gwadabe kuwa ya shiga tashin hankali mai zurfi. Hadiza ta riga data kaishi maƙura shi gani yake yi zai sauwaƙe mata kawai ya huta gudun kar watarana tasa ya aikata aikin dana sani. Yanzu jibi baƙin kishinta abinda ya ja. Suna isa asibiti aka karɓeta Dr sai faɗa take yi akan ya za'ayi irin wannan saken ɗinkin da akayi mata ya warware." Ɗakin sabuwar tiyata aka shige da'ita ga jini data zubar sosai. Wajen Malam duk suka ɗunguma suka je. Yana kwance kamar mamaci ko motsi bayayi. Duk mai tausayi inya kalli ɗakin da malam ke ciki sai ya zubar mishi da hawaye. Sun fi minti talatin a wajen kafin Yaya Tasi'u ya shiga wajen Dr ɗin Malam su kuma su Gwadabe suka koma ƙofar ɗakin tiyata. "Yanzu duk faɗan da akaima Hadiza bata ji ba sai da ta sake takalarka da wani jidalin? Wannan yarinya dai bata ji. Amman fa Gwadabe sai ka zama tsayayye sosai a gidanka kar ka kuskura kayi saken da kan yaranka zasu rabe. Wallahi matsawar haka ta faru Shikenan ni dai na faɗa maka. Kaduba gidanmu sai yanzu ne yake shirin farfaɗowa a haɗe kai. Tun su Yaya Tasi'u suna ƙananu ake abu ɗaya yau shekarata ni kaina nawa? Mata basa taɓa tsufa da kishi shine matsalar balle kace zasu watsar dan kansu. Barinma irinsu Hadiza masu zafin kishi. Itafa tun tana yarinya haka take da wannan baƙin kishin. Duk abinda aka siyo mana sai Hadiza tayi kuka in dai ba da ita za'a siyo ba. A makaranta akwai yarinyar da hadiza ta tsana kasan dalilin?" Auwala ya tambaya. Ajjiyar zuchiya ya sauke kana yace. "Sai ka faɗa" "Sabida yarinyar a ko da yaushe ita ke zuwa na farko a ajinsu. Daga ƙarshe sai da Hadiza ta ƙwace wannan ragamar ta hanyar nacin karatu da dena bacci sannan aka zauna lafiya. Kai itafa tafi kab ƙawayenta kyau bata ƙawance da wacce tasan ta fita dan masifa. Kai Gwadabe yake ta karkaɗawa yana sauraren Auwala tare da tunanin yadda zai shawo kan lamarin Hadiza. Lallai akwai gagarumin aiki a gabanshi to zaima iya gyara Hadiza kuwa, ko dai rabuwa da'ita shine a'ala a gareshi? Idanu ya lumshe kanshi na yi mishi zafi. A haka Yaya Tasi'u ya dawo ya tarar dasu jikinshi a mugun sanyaye da irin yanayin da yaga jikin malam ɗin. Shi kam ma har ya fitar da rai da tashin Malam. Almajiran malam kullum a cikin yi mishi sauka suke suma suna cikin wani hali. Likitane ya fito daga ɗakin da aka shiga da Hadiza a lokacin wajen biyun dare. Yaya Tasi'u da Gwadabe ne suka bi bayanshi har zuwa ofishinshu, ya basu waje suka zazzauna. "To mun samu nasarar sake yi mata ɗinki sabo. Tana buƙatar ƙarin jini dan ta zubar da jini sosai. Dan Allah a rinƙa kiyayewa koma menene dai ya faru a lura da'ita sosai tana buƙatar kulawa" "Doctor mun gode sosai. Zamu iya zuwa du mu biyun a gwada jinin namu in yayi to, akwai ƙaninmu a waje ma in namu bai kai adalilin abinda ake buƙata ba." A gurguje dai Hadiza kwananta biyu kafin ta samu ta farka hannunta ɗaure da ledar jini. Yaya Zara tana gefenta a zaune, sai Amaryar Malam. "Yaya Zara ina ƴata?" Da abinda ta soma kenan. Da sauri Amaryar Malam tace. "Zara maza kirawo likita. Sannu kinji Hadiza kai Allah mun gode maka" Yaya Zara ce ta miƙe ta je ta kirawo Dr suka tawo tare. Ya duba jikin Hadiza tare da yi mata tambayoyi" "Ku kula kar a bata abinci, sai tea ko kunu zuwa kwana biyu a kula. Sannu Allah ya ƙara lafiya' Idanu Hadiza ta lumshe hawaye suka zubo mata tana mai cike da nadamar yadda da auren Gwadabe. Data sani tun wuri ta fita sabgarshi yaje ya auri Shafa ita kuma ta auri wani mijin da yafi mata. Da Yaya Zara, da Amaryar Malam, da Hadizan ko wanne cikinsu da damuwar dake damunsu. Ɗakin ya ɗauki shiru na lokaci mai tsayi sosai kafin isowar Isuhu da matarshi da yara. "Isuhu kune a tafe?" Baiwar Allah ga waje zo ki zauna" Zama matar Isuhu tayi da ɗan goyonta a bayanta. "Sannu Hadiza ya jikin, ya kuma ƙarin haƙurinmu na Baba, ya jikin Malam? Ai daga can wajen malam ɗin muke kafin Auwala yai mana kwatancen nan ɗakin shi da maigidanki" A daƙile da wulaƙanci Hadiza tace. "Jiki da sauƙi. Haƙuri mun gode Allah " Yaran nata ta kalla daga kwance sun wani canja sun yi kyau sosai. Isuhu ne yace. "Amadu kuje ku gaishe da Mamanku. Hadiza sannu da jiki. Yaranne suka isa bakin gadon Hadiza ta riƙe hannun mai sunanta gam tana kallonta fes da'ita cikin kaya masu tsada. Gaisheta da jiki suka yi, tare da ta'aziyya. Su gwadawa ne suka shigo ɗakin. "Gwadabe kun dawo? Sannunku. Zara muje daga waje mu basu waje ko? Amadu Hadiza ƙarama kuzo muje" Amaryar Malam ta riƙe hannun yaran suka fice. Ɗakin ya rage daga Isuhu da matarshi. Sai Gwadabe da Auwala da Hadiza da take kwance. "Kiyi haƙuri ban kawo yara sunyi ta'aziyya ba. Bama nanne munje umara. Shi yasa, jiya muka shigo Maraɗi muka tadda labari shine muka tawo. Ga yaran su miki kwana biyu Furare zata zo ta ɗaukesu. Zan sa a kawo musu kayansu. Auwala yayi dariya yace. "Kako kyauta Isuhu sosai muna godiya da wannan zumuncin, baka duba halin gyatukarsu ba dan da an daka ta tata da zumuncin lalacewa zaiyi" Isuhu ya sosa kai yace. "Irin riƙon da Malam yayi mini shi kaɗai ka iya riƙe igiyar wannan zumunci ko da ban taɓa shiga rayuwar Hadiza ba. Mu kam zamu wuce Furare muje" Hadiza zamewa tayi tamkar mutum mutumi dan mamakin kuɗi da Isuhu yayi harda zuwa Umara. Yanzu yaranta sun taka ƙasa mai tsarki kenan, tare da ƙazamar Furaren data raina? Daman hausawa sukance ɗan hakin daka raina shike zamema gagara gasa. Auwala ne ya takama su Isuhu Gwadabe ya ƙaraso wajen gadon yace. "Yaya jikin naki Hadiza?" Banza tayi mishi ta tafi duniyar tunani dan batasan ma Gwadabe na tsaye a kanta ba. Shiru yayi kawai yana karantar yanayinta. Can Hadiza tace. "Tabb wai Isuhu ne ya je Umara shi da Furare, kuɗi yayi kenan?" Wannan zancan zuchiyane ya fito fili. Ringing ɗin wayar Gwadabe ne yasa ta juyo da sauri ta ganshi tsaye bisa kanta. "Bara'u kaddai har kun isa garin su Iyabo tsuntsun soyayya?" Da sauri Hadiza ta dubi Gwadabe shima ita yake kallo. "Gwadabe kai kaga irin ƙauyen da tsuntsun soyayya ya kai Iyabo kuwa. Haƙiƙa wannan tsuntsu bai mata adalci ba. Iyabo ta ƙare ta komaɗe ta zama bagidajiya sak. Yanzu haka ma tana asibiti ta haifi yaranta biyu du maza" Turus Gwadabe yayi yana sauraren Bara'u dake mishi bayani. Idanu ya lumshe a gaskiya baiji daɗin jin labarin Iyabo a haka ba. "Kana ji yarannan in aka barsu a wannan ƙauyen akwai matsala fa" "A'a Bara'u kar kace haka ka barsu kawai" Yana faɗar haka ya juya ya fice ya samu gefe guda suka gama tattsunawa da Bara'u. Daga nan ya fice a asibitin ma ya koma gida. Shafa na zaune tana hutawa Gwadabe ya shigo da sallama fuskarnan tashi cike da damuwa. Kwanciya yayi kawai yana kallon sillin damuwa da tunani sun caza mishi kai. Da sallama Shafa ta shigo hannunta riƙe da ruwan sha a kofin silba. "Jikin Yayanne kuma? Yanzu na gama girki kenan nake son zamu je ni da matar Mammada da matar Sabitu" Kuyi haƙuri gobe ba posting sabida akwai aiyukan turaren amare da aka bani kwangilar yi har show glass biyu manya, to kunga aikin da yawa. Masu son turare su tuntuɓeni ranar asabar zan turo kaya arewa nagode MRS BUKHARI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA UKU 20 ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke nannauya ya karɓi ruwan hannun Shafa tare da miƙewa ya kafa kai ya shanye tas ya sauke ajjiyar zuchiya. "Nagode sosai da kulawa Shafa. Jikin Hadiza da sauƙi harta farfaɗo tayi magana ma. "To Allah ya bata lafiya Alhamdulillah. In zubo maka abincinne?" "A'a bar abincinnan bakina babu daɗi sam. Ku hanzarta kuje ku kaima su Yaya Zara abincin." Shafa tace. "Da nace ko zan tafi da yarinyarnan a mayar da'ita wajen gyatumarta tunda ta farfaɗo? "A'a yarinyarnan ki ci gaba da shayar da'ita na baki ita halak malak horon da zanyi mata kenan. Idanu Shafa ta zare sai kuma tayi dariya kawai ta bar zancan jin sallamar matar Sabitu a ƙofar ɗakinta. A zuchiyarta ta tafi da niyyar bama Hadiza ɗiyarta. Ko da suka shiga sun tarar Yaya Zarah sai faɗa take yi ma Hadiza ita kuma sai hawaye take yi. Ganinsu ne yasa tayi shiru. Take jikin Hadiza ya sake rincaɓewa dole Shafa ta sake dawowa da wannan jaririyar. Kwanan Hadiza goma cib a asibiti aka sallamota da yammar ranar litinin sai gasu da kayansu sun shigo cikin gidan. Nan aka shiga yi mata sannu_sannu. Gwadabe kuwa tun ranar da Bara'u ya labarta mishi halin da Iyabo take ciki da irin rayuwar da take ciki bayan ya dawo Takai. Sai ya shiga damuwa mai tsanani. Ita dai Shafa a tunaninta sabida ciwon Hadiza ne. Amman sai take ganin abun yayi yawa, data tambayeshi sai yace mata kewar yara yake yi ne, kuma baya jin daɗi kwana biyu. A ranar Malam ya farka ya buɗe idanunshi sai dai baiyi magana ba. Ba shiri maza_mazan da matan Malam suka rankaya zuwa asibiti da surukan gidan matar Jamilu da matar Yaya Tasi'u. A asalin ɗakin jinya suka tarar da Malam idanshi biyu sai likitoci dake aune_aune a kanshi. Da idanu malam yake bin iyalinshi kawai, saida ya buɗe idanu ramarshi ta sake fitowa. Tasi'u ne ya matsa kusa gareshi sosai. Sai yaga bakin Malam na motsawa. "Tasi'u kamar fa Malam magana yake yi ko?" Cewar Baba Asshi. Jin haka yasa Tasi'u kara kunnenshi a bakin Malam. "Fhatsima ina Fhatsima take?" Abinda Malam yake furtawa a hankali kenan. Likitan malam yace. "Malam yana buƙatar hutu. Zaku iya fita tunda kun ganshi. Mutum ɗaya ya zauna dashi, ku ku fita.' Hutawa yake buƙata kar ayi hayaniya a kanshi. Kar kuma a lamince mishi yin doguwar magana dan Allah a kiyaye" Kai yasa ya fita. Iyalin Malam suka marama Dr baya. Tasi'u ne ya zauna a gefen Malam yana ta shafa sumar kanshi wanda hakan ba ƙaramin daɗi yake ma Malam ɗin ba. Da ɗaya da ɗaya iyalan gidan Malam sukaita shigowa suna duba jikinshi, a hankali cikin rashin kuzari yake amsawa daya gaji sai ya soma amsawa da ka. Hatta Hadiza saida ta zo ta duba Malam ta koma gida. Tana dawowa ta soma aikin girki, Shafa tace. "Yaya ke da baki da lafiya meye naki na yin girk? Ga abinci na kammala haar dake fa" "A_a riƙe abincin ki kiyi ta ci. Ai na warke ya kamata in karɓi miji ko Shafa?" Murmushi Shafa tayi tace. "To Allah ya ƙara sauƙi Yaya. Bari in miƙo miki yarinyar" Hadiza tayi mata wani banzan kallo kana tace. "Ai da kin barta wanda ya baki inya dawo sai ya karɓota ya kawo mun. In kuma ya bar miki itane huta roro, kinga na huta dama ke ya raina kece wahalalliya a wajenshi" Haɓa Shafa ta riƙe ita dai bata ce komai ba, dama wanki take yi taci gaba da wankinta. Ragowar yaran suna can cikin gida suna wasansu. Haka Hadiza tai ta kiciniyar girki. Matan gida duk wanda ya fito yaga tana girki sai yayi mata magana tare da cewa da'ita me yasa bata bari ba. Murmushi kawai take yi dan in tace zatai ta basu amsa zuchiyarta zata iya mata bindiga abubbuwane a zuchiyarta goma da ishirin. Tana zaune a gaban miya tana juyawa Shafa ta fito da jaririyar Hadiza ta ajjiyeta akan cinyarta tana bata nono tana kaɗa miya. "Kusun uwa, me zan gani haka Shafa ƴata naga kina bama wannan ƙazamin nonon naki gantalalle?" Shafa ta ɗago cikin dariyar cusa haushi tace. "Wallahi kuwa, ai mai gidanne ya bani ita halak_malak au wai baki ma da labari, ai ta riga ta cika cikinta dam da ƙazantaccen nono amman amintacce ingantacce a wajen mahaifinsu. Dan wallahi Gwadabe na ji da waɗannan nonuwan kasancewar ƴaƴanshi dashi ne kaɗai suka mayar da nonon haka. Ta ƙarashe tana dariya kamar ba magana ta faɗa ma Hadizan ba. Tana dasa aya taja dogon tsaki ta shige ɗaƙi tana ƙananun mita tare da cewa. "Mata sai jarabar tsiya ta hanani sukuni ta hana miji sukuni, wallahi yau ina daidai da ko wacce ƴar iska" Hadiza kuwa status ta zama tana tsaye sororo hannunta a sama a yadda ta nuna Shafa da hannun a haka Shafa ta barta. Karab kuma ta jiyo furucin Shafa. "Ke kika ƙyaleta kije ki rufeta da shegen duka ta gane akwai bambamci a tsakaninku" Cewar wani shashe na zuchiyar Hadiza. Ai kuwa ba tare da duba me kaje me kazo ba ta faɗa ɗakin Shafa da sauri. Karfa ku mance ga ɗinki sabo a jikin Hadiza yau aka sallamota daga asibiti. To mu tara a littafi na huɗu inda anan zan naɗe taburmar labarin in sha Allah. Shima fa akwai turka_turka me yawa a cikinshi mu dai je zuwa. Sannan kar ku mance akwai hutu kafin mu ɗaura da littafi na huɗun wanda zai zo muku da abubbuwan ban mamakin da zato bai zace su ba. Nagode ƙwarai. Gashi page ɗin yau babu yawa jiya na sanar muku ina aikin turaren amere show glass har biyu. MRS BUKHARI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Book 4 (1) MARAƊI Asibiti:. Tasi'u yana zaune a gefen malam hannun su yana cikin na juna tamkar abokai. Malam na ji da Tasi'u fiye da duk wani ɗa daya haifa, haka yake ji da Baba Fhatsima fiye da duk matan duniya, yake kuma jin tausayin Hadiza fiye da sauran yaranshi. "Allah ya jiƙanki Fhatsima. Tasi'u!" Malam ya ja sunan, Tasi'u yace. "Na'am Malam akwai abinda kake da buƙatane?" "Gani nake yi kamar baƙin cikin gidana da baƙin cikin matanane yayi sanadiyya Fhatsima, ji nake kamar ni nayi ajalinta" "A'a Malam ko ɗaya kai da gidanka ba zaku iyayin ajalin Baba ba. Lokacin mutuwarta ne yayi, kayi haƙuri ka kwantar da hankalinka. Sannan Malam babban albishir shine yanzu abinda keke nema da mafarkin faruwarshi ya samu. Ahalinka sun haɗe kawunansu kowa yana zaune da ɗan uwanshi da zuchiya ɗaya mun haɗe kawunanmu mutuwar Baba Fhatsima ta ratsa zukatan ahalinka Malam. Shin ko da iya wannan ba zaka kwantar da hankalinka ba ?" Idanu Malam ya lumshe zuchiyarshi sai yaji ta ɓangare guda tayi sanyi, ta ɗaya ɓangaren kuma sai mutuwar matarshi ta sake dawo mishi sabo fil. Hadiza:. Shafa na zaune taga Hadiza ta shigo da sauri. Tana isowa kusa da'ita sai kawai ta rufeta da dukan da yaba Shafa mamaki. Jin kafafniyar dukan da Hadiza take yima Shafa ne da faɗin "kar ki je ɗinkinki ya sake ɓallewa Yaya" Yasa matan gidan fitowa kusan mutum huɗune suka shigo ɗakin suka jaye Hadiza tana haki. Duk da sun sha dambe Hadiza ta doku da kyau a hannun Shafa, take Shafa jini ya soma bin ƙafarta halamun ƙaramin cikin dake jikinta ya zube. Duk da haka bata bar Hadiza ba "Wallahi sai kinyi nadamar wannan faɗan da kika takalo. Na dena ragar miki tunda dai ke jahilace mai kishin hauka wawuya marar tunani" Wannan furuci yafi komai ɗaga hankalin Hadiza ainun. Yau ita Shafa ta kira da suna jahila? Jan hannunta matar Mammada tayi ta mayar da'ita ɗakinta. Sai ita ta ƙarashe mata girkin nata ta shigar mata dashi ciki. Ciwo ya dawo mata sabo Ita dai tana kwance ta mugun ƙurama silin idanu, damuwa sun ƙara cunkushe mata zuchiyarta. Ga a Irin wadatar da ta ga Isuhu da matarshi abun ya sosa mata ranta, bawai baƙin ciki take yi mishi ba, ba wai finta matarshi tayi ba ko ɗaya itama tasan mijin da take aure babu raini. Ga Gwadabe yanzu shigar shaddajo masu tsada yake yi sabida yana harka da manyan masu kuɗi sosai, sana'ar magungunanshi tana mugun kai mishi sosai. Ajjiyar zuchiya ta sauke da jiyo muryar Anty Badi'a ta shigo da yaranta suna biye da'ita. "Hadiza ashe ke dai baki da hankali ko? Wallahi kibi lamarin kishi a hankali. Akan Gwadabe dai kike wannan wautar kuma kinsan bazai goyi bayanki ba sai ma yin Allah wadai da abinda kika aikata, gashi a garin shirmenku cikin Shafa ya zube. Kika sake yayunki suka ji abinda kika aikata ranki ne zai ɓaci kinsan Sabitu duka zai yi miki sakarar kawai. Yaran ta barma Hadiza ta yi ficewarta ganin yaran yasa Hadiza haɗiye yawu ta haɗiye damuwarta tace. "Kuzo ku zauna mana ko guduna kuke yi? Babban yace. "Mu gida muke son a mayar damu wajen Babanmu mu ba zamu zauna ba" Gaban Hadiza ya faɗi data ji abinda yaron yace. Ta kuma tuno da roƙon da Isuhu ya dinga mata akan lallai ta tafi da yaranta taƙi fur a ƙoƙarinta na ƙuntatama Amarya tare da kawo musu cikas a cin amarcinsu. Ashe batasan cikinta ta daɓa ma wuƙa ba ita bata sani ba. Ajjiyar zuchiya ta sauke tace. "Kuyi haƙuri kunga dare ya rufa gobe za'a mayar daku gidanku. Kai usmana kaje banɗaki ka yi alwala maza kaje waje kayi Sallah. Ke kuma inya fito sai kije ki ɗauro alwala kiyi sallar anan sai in zuba muku abinci kuci." Ficewa Usmanu yayi, yana fita sai ga Ummi ta shigo ɗakin anyi mata wankan yamma Abba na biye da'ita. "Kai maza jeka ɗakin uwarka karka kuskura ka zauna mun a ɗaki ɗan iska mummuna mai ƙaton kai irinna ubanshi" Abba ya fashe da kuka ya nufi hanyar waje. Ashe Gwadabe na tsaye a bakin ƙofar ɗakin a kunnenshi duk tayi wannan zagin. Abba ya raɓa ya wuce uban da gudu. Kallon kallo ne ya wanzu a tsakankanin Hadiza da Gwadabe. Kai ya girgiza kawai ya saki labulen ɗakin ya dawo falo. Ledar hannunshi ya ajjiye a gefe yana shirin fita usmana ya shigo. Yaron yabi da idanu harya shige uwar ɗakin, har ya sa ƙafa sai fita shi kuma daga falon sai ya dawo dai. Labulen ya sake ɗagawa Hadiza na tsaye tana zirga_zirga tana naushin hannunta. "Yarannan kafin in dawo su bar ɗakinnan dan ban amince su zauna mun ba suna da gidan uba dan ubansu a mayar dasu In kuma kina sha'awar komawa kan ƴaƴanki ne ƙofa a buɗe take zaki iya sanar dani kinga gashi yayi kuɗi" A tsorace Hadiza tace. "Me kake nufi danine? "Bala'i da masifa nake nufi dake. Ke baki sanni bane amman zan nuna miki wallahi nafi ƙarfin gidana kuma ni gidana bazai zama sansanin yaƙi da ƴan ubaba ki sani. Na fiki iskanci da bariki, baduniye ne da kike ganina. Da irin faɗa da tsawar da Gwadabe yake magana ya tsorata Hadiza dan tayi imanin na tsakar gida ma na iya jiyo sababinshi balle Shafa da ga_ ɗaki ga _ɗaki. Labulen ya sake a zafafe ya fice. Yana zage_zage Haka dole Hadiza ta kama hannun yaran ta kaisu ɓarayin Anty Badi'a tare da mata bayanin abinda ke faruwa" "Ai yayi kyau dama mai haƙuri bai iya fishi ba, maza dai ki turkuɗe auren naki ki huta kinga sai a buga miki tambarin ga wacce kishi yake hanawa zaman aure. Kuma Malam kinsan zaifi fishi dake ainun. Ga Sailuba nan ta kula dasu ni asibiti zanje in kaima Babansu abinci in sake dubo Malam ance jikinshi da sauƙi har yana magana." Ajjiyar zuchiya Hadiza ta sauke a sanyaye tace. "Allah ya bashi lafiya dorarriya kya gaisheshi da jikin in kika je." A daddafe Hadiza ta koma ɗakinta ta shiga ta tadda Gwadabe zaune yana cin tuwon Shafa yana ba Abba da Ummi a baki. Ko kallon inda Hadiza take baiyi ba, itama wucewa tayi abunta ciki bata sake fitowa ba sai washe gari da asuba. A falon ta tadda shinfiɗar bargon da take da tabbacin na Shafa ne harda matashin kai. Kai ta girgiza kifiyar kishi ta soketa. Cikin wannan gaba har kwana huɗu Gwadabe na abu ɗaya baya cin abincin Hadiza, baya kwana a ciki sai falo ko gaisuwarta baya amsawa, ga yawan waya da yake yi da Bara'u akan Iyabo harda kuɗaɗen da Gwadabe yace aima Iyabo siyayya Hadiza ta sani, a ranar kasa bacci tayi sai juyi kawai ta riƙa yi har gari ya waye, ta kuwa tashi da ciwon kai mai tsanani, abu ya haɗe mata goma da ashirin. A haka har aka sallamo Malam daga asibiti ya dawo gida ya tarar da abun farin ciki yau ga yaranshi kawunansu a haɗe har an zauna zaman meeting na lumana na farko tare da sake ma juna ta'aziyyar Baba Fhatsima. Yaya Zarah dai da aka gama komai sai ta yi ma kowa sallama ta tattare yaranta suka koma. Hadiza har zuwa wannan lokacin a cikin faɗa suke da Gwadabe ɗiyarta dai tana hannun Shafa, ta kasa tambayar Gwadabe ɗiyarta, ga wajen da akai mata tiyata sai ciwo yake yi mata. Da dai taga abun Gwadabe bana lafiya bane ranar daya dawo ɗakinta ta fito da zummar yi mishi magana ta riskeshi yana waya da Bara'u Sakina ta haihu. "Ah masha Allah to Shikenan zamu tawo kafin suna ko da ni da Shafa ne Hadiza jinya take yi kaga ba tayi doguwar tafiya ba. Kace ina ma Sakina sannu, kaga in muka zo sai mu tawo dasu Toye" Sukaita hirarsu Gwadabe ya dinga jan hirar dan ya baƙantama Hadiza daga ƙarshe dai dole sukai sallama. "Dama dan Allah nazo in roƙeka gafarane a bisa abubbuwan da sukaita faruwa. Sharrin shaiɗanne kuma hakan ba sake faruwa zaiyi ba ni wannan fishin ya isheni" Ƙur Gwadabe yayi mata da idandunanshi yana wani ƙanƙancesu, ita kuwa kanta a ƙasa tana jiran me zaice. "Hmm Hadiza kenan sai yaune kika ji kina son kizo ki bani haƙuri, ai nayi tunanin kinfi jin daɗin zamanki a haka? Harni zaki cema yarona mai ƙaton kai kamata dan iskanci da wulakanci, kina so tun suna yara ki cusa musu mummunar aƙida. Sannan kika dubi tsabar idanuna kika kirani da azzalumi mayaudari mai bibiyar matar Aure " Da sauri Hadiza ta runtse idanunta tare da katse Gwadabe ta hanyar cewa. "Yaya ni dai dan Allah ka yi haƙuri banda tashin tashina" "Rufa mun baki saina gama tsab" Dole ƙanwar naƙi Hadiza ta rufe bakinta ruf Gwadabe yaita tambotsai kafin daga bisani yace ya haƙura amman fa ba har cikin zuchiyarshi ba. "To yarinyar kuma sai yaushe za'a dawo mun da'ita?" Dariya yayi yace. "In dan sabida a dawo miki da yarinyane kika zo ban haƙuri kinyi gwari Hadiza. Yarinya ai kin nuna bakya sone shi yasa kika so ta mutu ki huta. Aikin banza aikin wofi" Ya faɗa tare da tashi yayi ficewarshi sallar Isha. Har gwadabe ya dawo Hadiza na ciki tana kuka, ko daya dawo bai ko nuna ya damu da ganin Hadiza a wannan yanayin ba. Amman a ƙasan zuchiyarshi ya tausaya mata, ga rashin uwa, ga ciwo a jikinta, amman daya tuno halin jarabarta sai yaji haushinta. "Har yanzu baki dena wannan kukan ba wai Hadiza, ko dukanki nayi ne, wannan wanne irin buyagine?" Hadiza ta jima tana ƙoƙarin haɗiye kukanta yaƙi haɗiyuwa sai dai da taci nasarar karya zuchiyar Gwadabe. Hannu yasa ya ɗagota ya mannata da ƙirjinshi ya shiga shafan bayanta. Sun jima sosai a haka ji yayi sonta na ratsa jikinshi. Amman a kashi ɗari na sonta saba'in ya zube tas "Ya'isa haka bani abincin to inci." A kunne yayi mata raɗar, murmusawa tayi taje ta ɗakko mishi abincin ta kawo mishi, kanta na kan cinyarshi yana cin abincin yake cewa. "Gobe zan shiga Damagaran akwai wani babban mutum da aka haɗani dashi zan kai mishi maganin ƙarfin maza yana da rauni ta fannin gamsar da iyali, kuma yayi maganin harma ya gaji. Ga arziki amman babu mace ko ɗaya a gidan duk sun kama gabansu. Shine akayi mishi hanyata gobe zanje sai ki saka ni a adda'a kwana biyu zanyi a gidan nashi akwai dafe_dafen magani da zanyi, in dai yasha da izinin Allah sauƙi zai samu, ki taya ni da adda'a" Murmushi Hadiza tayi tace. "Yana son ya zama jarumi kamarka kenan?" "Au ni jarumine bani da labari?" Ya tambaya yana shafa sumarta. "Me abu da abunshi kura da kallabin kitse. Kullum fa saika ɗibgi magani muna gani" Dariya yayi sosai ya kawar da zancan da cewa. "Sakina ta samu kai yau ta samu ɗiyarta mace. To ana gobe suna in jikinki ya sake yin kyau sai mu rankaya dukka, in kuma baiyi ƙwari ba sai muje da Shafa da yaran duka. Su Toye ma sun dawo daga wajen Gyatumar tasu suna Takai saiki soma shiri ko?" "Allah ya nuna mana lokacin" "To Ameen " Daga haka dai faɗa ya ƙare washe gari Gwadabe da hannunshi ya ɗauko yarinya daga wajen Shafa ya damƙama Hadiza ita, yai musu sallama ya tafi. Kafin ya tafin saida ya ba ko wacce wadataccen kuɗin tsaraba, ya shiga ya duba Malam yai mishi sallama ya kama hanya. Nan su Shafa suka shiga shirin tafiya. Tsakanin Shafa da Hadiza gaisuwace kawai itama gaisuwar bata girmamawa kamar yadda Shafa ta saba Yaya sama Yaya ƙasa ba, ana dai gaisuwar a hakanma Gwadabe ne yai ta tausarta. Ita kanta Hadiza tasha jinin jikinta dan hatta su Yaya Tasi'u basa amsa gaisuwarta kuma suka sanarma Malam abinda Hadiza ta aikata. Ya dirar mata da faɗa Baba Asshi da Baba Suwaiba, da Amaryar Malam duk sukai mata faɗa akan kuskurenta. Malam yasa akai mai kiran Shafa ya bata baki ya bata baki sosai. "Babu komai Malam wallahi ya riga daya wuce" "To Allah yayi miki albarka Shafa'atu, ina su Abba?" Ɗan murmushi tayi tace. "Suna ƙofar gida makaranta" Sallama tayi mishi ta komawarta gida, ta shiga aikin girki, Hadiza ma aikin girkin take yi na tarbar Oga, matan gidan ko wacce na aikinta anata zuba hira abun gwanin ban ƙawa. Daf magriba sai ga Gwadabe ya shigo da niƙi_niƙin kayan tsaraba. Daga ƙofa ya zunguri Shafa da ledar lemo da ayaba. "Riƙe nan inna dawo sallah ki sameni a ɗakin Hadiza mu tattauna" Ta amsa tayi godiya, ta ajjiye ledar ta shige banɗaki, shima alwalar yayi ya tafi masallaci a gurguje dan har an tada Sallah. Sai da Shafa ta sake gyara kwalliyarta dan yanzu a fice take ta ɗauki shawarar wata ƙawarta abokiyar aikinta data ziyarceta washegarin ranar da Hadiza ta bita har ɗaki. Ba iyaka Gwadabe Shafa ta ɗaga ma hankali da kwalliyarta ba harda Hadiza dan kusan tafi Gwadabe firgita. Ga gashinta sai sheƙi yake yi, gashi dai shi ba yawa ba amman ta gyare abunta tsab gwanin sha'awa. Zama tayi a gefen Gwadabe jikinsu na gugar juna, Hadiza na daga ɗaya ɓangaren. "Barka da dawowa ya hanya, da fatan abinda akaje nema an samo? Barka da gida umman Ummi" Saroro Hadiza tayi tana kallonta tama gagara amsa sannun da take yi mata ta bita da idanu kawai. "Sannu Shafa Irin wannan kyau haka. Ina Iyabo kika barota ?" "Iyabo tayi bacci shine na shinfiɗeta a kusa da Abba" Da yanga take magana. "A_a _a_a je ki ɗakkota inta farka tana neman nono fa? Maza jeki ɗakkota bana son abinda zai taɓa Iyabo" Har Shafa ta fice ta dawo tsakanin Hadiza da Gwadabe babu wanda yace komai. Shinfiɗe Iyabo Shafa tayi a kujera. "Hadiza zuba mana abincin yau dai muci tare sai in rarraba muku tsarabarku data yaran ko?" Fuska a turɓune Hadiza ta zuba musu lafiyayyen tuwo da miyar bushasshen karkashi wanda yaji naman ragon suna da kayan ciki. Tsakankanin Shafa da Gwadabe ne kawai suke ta hirarsu har aka kammala cin abincin dai. Atampipi da leshi ya zaro a ledarshi ya ajjiye a tsakar ɗakin. "Wannan naku ne da zaku dinga kuyi fitar sunan Sakina. Gashinan kala uku_ukune ke Hadiza tunda kece babba ki soma ɗauka" "Itama babbace ta ɗauka ta bar mun nawa" Shafa tasa hannu ta zaɓi ta darje tace. "Mungode Allah ya ƙara arziki" Leda ya miƙoma Shafa yace. "Wannan nasu Abbane gashinan kinmun ƙorafin Abba bashi da wanduna kwanaki, to ga wannan a ƙara mishi dashi. Hadiza kema ga na su Ummi, wannan kuma na sabuwar jinine. Hadiza ta karɓa tana bin manyan laidojin da Gwadabe ya bama Shafa. Ta kalli ta hannunta ta gyaɗa kai kawai. Tace angode wallahi ta kasa dan wani ƙududune ya tokareta a wuya. Shafa kuwa sai adda'a take yi mishi. Ya haɗa musu da dubu shida_shida. "Wannan kwa yi dinki. Ragowar kayannan Hadiza ki ajjiyesu a wajenki na Sakinane sai ku ƙara da taku gudummawar. Ke Shafa ɗauki Iyabo bari in ɗebar miki kayan in rakaki" Hakan kuwa akayi, suna fita Hadiza ta wuce ciki fu tayi kwanciyarta. Ko da Gwadabe ya dawo yayi mata magana tayi watsin ruwan tsarki dashi, shi kuma yayi tunanin ma bacci take yi. Gaga_gaga har ranar tafiya Takai yayi sukai ma jama'ar gida sallama suka tafi. Da daddare suka shiga Takai Bara'u na ƙofar gida ya gansu. "Gwadabe kune a tafe? Maraba lale da zuwa. Hadiza, Shafa bismillah ku shiga ciki' Bayan an gaggaisa sai suka wuce ciki Gwadabe kuma yayi zamanshi wajen amininshi tunda yana jiyo muryoyin mata a gidan. "Ya bayan rabuwa Bara'u. Ya labarin Iyabo da rayuwar gidan aurenta?" Dariya Bara'u yayi yace. "Kai Gwadabe maimakon ka soma da tambayar yara da noma kamar yadda ka saba sai ka somamun da batun Iyabo? Nasan ana binka sallah ga buta yi alwala kayi Sallah. "Haram munyi sallolinmu dukka a hanya. Kai dai bani labari" Ajjiyar zuchiya Bara'u yayi fuskarshi ta sauya. Yace. "Labarin tsuntsun soyayya babu daɗi. Ga wani babban al'amari daya faru a gidanku wanda duk garinnan na Takai anata tsogumi akan abun Gwadabe. Nasan baka sani ba Gwadabe. Yanzu haka Babala tana asibiti rai a hannun Allah. Tashin hankalin da take ciki ya kai. Mrs Bukhari ce Ayi haƙuri da wannan idanun nawa bai warke ba. Sannan dan Allah ba kullum zan dinga posting ba sau uku a sati zaku dings samu sakamon idanuna daya matsa mun da ciwo nasan zaku yi mun uzuri in ku kai la'akari da ni bana wasa da typing sam. Nagode. Ku taya ni jaje Allah yayi ma magena rasuwa mai suna Sameer jiya. ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU (2) IYABO:. Da guduna na nufi Cubu na ɗagata tsaye ba sai jini ya yanke mata ba. Kishiyoyinta dukka suka ruɗe. Baku da imani amman yarinyarnan kasheta ku ka yi niyyar yi, ku ko ganin girmanku bakwa yi ne? Sannu Cubu muje daga inuwa" Najata na kaita baranda jini dai bai tsaya ba a haka mijin nata ya shigo ya samemu numfashinta ma lokacin ya bar gangar jikinta, kishiyoyin duk sun tsure. Shikenan ta mutu kun kasheta kun huta kishi ya ƙare bar maku gadin duniyar" Carab mijin Cubu yace. "Wani abun suka yi mata ne ni ban sani ba?" Shigowa nayi na samesu sun zauneta suna son su kasheta ita da abinda ke cikinta dan rashin imani" Ni da mijin Cubu muka kinkimeta muka yi waje da,ita a haka a sume aka hau mashin da ita har zuwa Girai ba shiri aka bata gado duk mun ruɗe muna cikin tashin hankali ni kam hawaye kawai nake yi. "Waye mijin yarinyarnan da aka shiga da'ita ɗakin haihuwane?" Yayi zuruf ya miƙe. "Ganinan?" Likitan ya ƙare mishi kallo dattijone fa babba, ita kuma Cubu irin fulaninnanne sirara kamar Yaya Hamma ga karancin shekaru." "Shin ka taɓa barinta taje awon ciki kuwa?" Da tsoro sosai a fuskarshi yace. "A gidana ba'a zuwa asibiti kwata_kwata itama dan kishiyoyi sun so halakata ne shi yasa na amince muka tawo" Ajjiyar zuchiya ya sauke likitan in da sabo ai ya saba da ganin fulani da ɗabi'unsu iri iri. "Hannu zaka saka mana yanzu anan. Baiwar Allah kamar ke zaki fi fahimtata tiyata za'ayi mata domin a samu a ceto ran ɗaya kar a rasasu duka" Mijin Cubu dai yaƙi saka hannu sai ni nasa hannu aka shiga da'ita ɗakin tiyata. Sauƙin da aka samu ya biya kuɗin duk abinda ake buƙata. "Ni zanje in sanar a gida, sannan a turo wacce zata taimaka miki wajen kula da'ita. Sannan zansa yara su kawo kayan jaririn" Da kwaɓaɓɓiyar hausarshi yayi magana kafin ya tafi ni kuma na samu waje na zauna sai tubka da warwara nake yi. Wannan rayuwa ni ta isheni wallahi komai ya fice mun a kaina, ni rayuwarma banƙi ace ta tsaya ba aima kowa hisabi ya kama gabanshi. Wai me mata suke son zama ne a rayuwarnan akan kishine?" Idanuna na lumshe wasu hawaye suka zubo a kumatuna. A haka babban yaron mijin Cubu ya kawo kayan jarirai cikin ghana most go, ya bani kuɗi nera dubu uku yace in riƙe ko za'a buƙaci wani abun. Yana tafiya na miƙama ma'aikatan jinyar kayan suka shiga dashi, ni ko dubawa banba. Cikin awa uku akaima Cubu tiyata likitan ya fito. "Alhamdulillah mun samu nasarar ciro abinda ke cikin nata yana cikin ƙoshin lafiya Namiji ne. Ita uwar itama tana cikin ƙoshin lafiya, sai dai muna da buƙatar jini leda biyu da za'a ƙara mata" Hamdala nayi na godema Allah, na sake godema Allah. "Likita a ɗebi jinina in zaiyi a saka mata" Jim yayi yana nazari kamar bazai yarda ba dai sai kuma ya amince. Muka je aka ɗebi jinina akayi gwaje_gwajen daya dace da aka tabbatar da lafiyarshi sai suka ɗibi leda biyu. Amman nafi awa ɗaya a kwance ina hutawa kafin na tashi na goya biyu na fito. "Yafendo na gani, da matar Babansu Baɗɗo a zaune a benci" "Yafendo kun iso kenan?" Yafendo ta miƙe tace. "Nuna mana ɗakin da Cubun take, munfi minti talatin da zuwa ai munata zaune" Kafin in basu amsa sai ga ma'aikata jaye da Cubu a gadon marasa lafiya zuwa ɗakin hutawa. Dasu muka ɗunguma muka shiga, jarirai wasu na kuka, wasu na bacci, wasu suna kwance shiru. Jaririn Cubu ma yana kwance sai bacci yake yi kanshi duk suma. Likitane akan Cubu yana ɗaura mata ledar jini. Matar Babansu sai wani hararata take yi tana wani fiffiƙa, komai itace akan gaba sai zaƙewa. Daga can gidan Babannasu aka kawo mana tuwo. Dada ma ta aiko mana da shinkafa da miyar da nayi mata. Nan matar Baban ta kasa haƙuri saida ta riƙe bakinta. Haka dai muka wuni cur sai zuwa dubiyar Cubu akeyi. Da magriba sai ga Baɗɗo, Yusufu, da Daso sun shigo. Daso harda filas ɗinta na ruwan zafi cike da shayi mai madarar luna. Naso in kwana a asibitin Yafendo ce taƙi yarda haka nabi su Baɗɗo muka koma gida. Nan sintiri ya auremu kullum muna tafe dai har aka sallamota . Kishiyoyinta kuwa babu wacce tazo dan tsoron abinda suka aikata. Mu sai daga baya ma muke jin labarin ya korasu gida bisa laifin da suka aikata. Allah cikin ikonshi sai mijin yace a wuce da'ita gidan Dada. Munyi farin ciki sosai amman wallahi ko kwana guda batai ba mai nagge yazo da kanshi ba aike ba ya tusata a gaba . Muna ji muna gani gidan suka je suna ni kam banje ba an dai kawo mun abinci da naman suna dai. Banma sake sa Cubu a idanuna ba har saida sukai arba'in suka zo mana yawon arba'in ɗin. Yaronta yayi ɓukeke dashi sosai gata ƴar firit da'ita sabida fargaban tsotso duk saita sake suɗewa" "Kin rame sosai ko bakya samun abinci kina ci ne Cubu" "A'a Adda inaci, kawai zaman gidanne ya isheni so nake in koma. Mugunta suke yi mun, kuma ko Baban yaronnan ya kawo mun abun daɗi dasu da yaran gidan suke cinyewa. Kuma Baffa ko batun komawata bayayi. Shima Baban yaron inna tambayeshi yaushe zan koma, baya iya bani amsa sai inga ranshi ma ya ɓaci Adda" Kai na gyaɗa nace To ko dai wani abunne, ko kuma wata kitimirmurar kishiyoyinki suka ƙulla miki. Amman kina yin addu'o,in da nasa kika haddace?" "Inayi sosai Adda, kuma ina yawan ambaton la'ilaha, illah, anta, subuhaka kuntu minal zalumin, sai in ƙara da hasbiyallahu, la'ila,illah anta, alaihi,tawakkaltu,wahuwa rabbularshirazeem." Yauwa da kyau ki riƙe kiy ta nanatawa Allah zai kareki daga sharrin masu sharri. Zanci gaba da yin makaranta amman a gidan Dada zan dinga yi da daddare, kafin ki tafi saiki dinga zuwa. In kin koma ma in mijinki zai barki ki dinga zuwa sai ki dinga leƙowa ai" Haka muka wuni muna hirarmu, da yamma sai ga Khari ta leƙo, kafin ma ta zauna sai Baɗɗo itama ta shigo. Nan muka buɗe sabuwar hirarmu ta zumunci. Harga Allah ina jin farin ciki sosai inna ganni a cikin dangin Dada, ina matuƙar son Dadane. Gaga_gaga muka komar da karatunmu zuwa gidan Dada. Inna gama dasu Baɗɗo da Amaduyal sai in koma wajen Dada itama in mata ƙari a Qur'ani. Nayi iyakar yina dan ganin na koya ma Dada baƙi amman dai ta kasa koya, sai muka haƙura nake yi mata Qur'ani da hadisi. Su Baɗɗo kuma Qur'ani, hadisi, da koyoon baƙi nake yi musu. Cikin sati guda ba sai makaranta ta girma ba, maƙotansu Dada duk suka shiga makarantata ina koyar dasu inajin nishaɗi, in sati yayi su bani kuɗin laraba nera ashirin_ashirin. A cikin sati uku na tara ɗalibai talatin cib duk sati ina samun kuɗin laraba nera ɗari biyar banda su Baɗɗo. A cikin sati na huɗune nake sanar dasu zanje birni amman bazan jima ba in sha Allah. Gaga_gaga na shirya tafiyata ranar talata na shiga Kano da tsaraba rigi_rigi kai tsaye gidan uwani na yada zango. A tsakar gida na tarar da kishiyarta tana wanke kayan jarirai, Ummi ƙanwar uwani kuma tana wankin kayan jini. "A'a Anty Iyabo har kinzo? Ko dai tun tana nakudar ta kiraki a wayane?" Cewar ummi da tazo ta tarbeni. Ta sauka kenan? Ni da ƙauyenmu ba sabis ya za'ayi ta kirani ranaku kawai na kintata na tawo. Yaushe ta haihu?" Kishiyar Uwani ce ta katse mana hanzari ta ganyar gaisheni a turɓune. Fuskata a sake na amsa mata ni da ummi muka rankaya ciki. Hajiyansu Uwani na ciki ita da Hafizun. "Iyabo kece da magribarnan maraba" Wallahi kuwa Hajiya. Saina taki sa'a ashe ta sauka?" "E ta sauka, zauna ga ƴar taki ki ɗauka, bata fi minti talatin da haihuwar ba, ita ko wanka batai ba" Zama nayi na amshi yarinyar tubarkalla da'ita ga hanci. Gaisawa muka yi da Hafizu sai naga ba yadda muka sababa. Hajiyace ta katsemun tunanina ta hanyar cewa da Hafizu. "To ya rage a tsakaninka da Uwani Hafizu. Ta riga data haihu idda dai ta ƙare. Sai kaje ku sasanta inta amince maka sai a sake sabon ɗaurin aure. Ni kam tunda Iyabo ta iso zan tafi" Hajiya ta tashi ta fice. Ni wallahi mamaki ma ya hanani yin sallama da Hajiya. Uwani kawai nake kallo, ita kuwa sai shan shayi take yi a ƙaton jug. "Iyabo tunda Allah ya kawoki komai zai zo da sauƙi nasa. Kuskurene ya shiga tsakaninmu da Uwani har takai da na furta mata kalmar saki. To Allah cikin ikonshi ɗazu ina tasha ana mun lodi sai kawai sanarmun da haihuwarta akayi. Kinga idda ta sauka a kanta. Ki tayani bata haƙuri ni ko nawa take so na sadaki zan nemo in bata. Inma so take yi in yi mata akwati wallahi zanyi" "Iyabonce zata sa in koma sabida uwatace? Ai wallahi kama ji na rantse na gama aurenka kenan. Kuma yara zasu koma hannunka babu yaron da zan riƙe. Daɗine ma yayi maka yawa in ciyar da kaina da yarana, in biya musu kuɗin makaranta akan mitsiyaciyar matarka mai kama da bulugari Ni Hafizu ka jefa da kalmar saki. Ai aure da kai har duniya ta naɗe. Gashi can za'a shiga sallah kayi da jiki" Kasaƙe ni dai na kasa magana. Tashi Hafizu yayi yana sharce zufa har ya kai bakin ƙofa yace. "Iyabo ki taimakeni. Wallahi inason Uwani. Jarabarta ce duk taja mana. Jeka Hafizu zamu tattauna in sha Allah za,a samu haske" Godiya yayi mun ya fice. Uwani kar kiyi haka. Ki tuna Hafizu na sonki sosai. Sannan ki duba yara" "Iyabo in kina so ƙawancenmu ya cika. To ki kaso aurenki kizo ki maye ma Hafizu gurbina mana. Ni ba tsuntsun soyayya bace da soyayya za tai ta jan rayuwata kamar ke da kika zama bagidajiya ba Jibakki yadda kika dawo fa ruwan kwara_kwara. Ni bana ma son namiji mai nacin soyayya kin ganni inason a dinga barina in samu sarari, ba ko da yaushe nake son takura ba.' Leƙowar ummi ce ta katse Uwani. "Anty an kai ruwan wankan kije kiyi" Fita Uwani tayi, ni dai nayi jigum sai ga kishiyar Uwani ta shigo da kulolin tuwo dana miya, harda gaushi. Itama da ciki a jikinta. Ajjiyar zuchiya na sauke na ajjiye yarinyar a gado na sakko da su Hassan duk bacci suke yi na shinfiɗesu na fito. Alwala na ɗaura na koma ciki, na tadda kishiyar Uwani na zaune tana cin tuwo. Ina kan rama sallolina Uwani ta fito wanka. Sallamar sallar magriba nayi wacce tayo daidai da shigowar Hafizu ya nemi waje ya zauna harda leda a hannunshi cike da balangu. "Gashi kici ki sha tea, gobe zan shigo da kayan tea ɗin. Ke kuma in kin gama sai mu tafi ko?" Yace da matarshi. A_a Hafizu ku dukka ukun inaso zanyi magana daku. Domin na fahimci kamar akan amaryarka ne aka samu wannan saɓanin" Ai sai ya gyara zama yace. "Alaja kinga maganarnan a batta kawai babu abinda zata haifar sai fitina. Kuskurena ɗaya na sakinta da nayi ne" "Sabida kana baƙin ciki da ɗaukakar da Allah yaimun akan kasuwanci ba. Hassadarka harta fito fili Hafizu na gama zama da kai Allah shine shaidata nayi iya yina. Iyabo na roƙeki da girman Allah karki tursasani komawa gidan Hafizu ki barni in auri wanda a ƙalla ko abincine zai iya bani. Wahalar Hafizu waccece ni Uwani ban shaba. Ke kuma ki ficemun daga gida kar in sake ganinki a gidana. Yaranku zuwa anjima in suka dawo daga gidan Hajiya zan rakosu da kayansu kije ki haɗa da ubansu kiyita rainonsu gaki ga rijalu tsohuwar makira" A zafafe kishiyar Uwani ta tashi ta fice harda doka tsaki dogo. Uwani ta bita da manyan ashariya ba sai faɗa ya tashi ba gaga_gaga da ƙyar ƙurar ta lafa wallahi Uwani dake jego itace har waje wai zata daki kishiyarta sai maƙota aka jayeta ta shiga. "Da ki tsaya mana kiga. Tsohon mitsiyaci saika bita ai." Ni dai da ƙyar na dinga jan Uwani har cikin gida. Hafizu na koma na samu a waje yama kasa tafiya. Hafizu kayi haƙuri ka ɗan ɗauke ƙafarka zuwa ɗan wani lokacin inta huce. Kafin in koma zanyi iya yina" Murmushi yayi yace. "Alaja karki ɓata yawun bakinki in dai ta balbalin ce ba zata dawo hannuna ba. Ki mata godiya a bisa halaccin da taimun Uwani ta zauna dani cikin baƙar wuya. Bana mance sanda take fita ta nemo mana abinda zamu ci. Sannan bana mance sanda talauci yasa ni da'ita duka muka bar ƙasar dan neman rufin asirin kanmu dana yaranmu. Iyabo kice mata Nagode ƙwarai Allah ya bata miji nagari wanda zai tausaya mata" A wajen ya tafi ya barni. Kai na girgiza na koma cikin gidan. Gaga_gaga haka muka wayi gari cikin hukuncin Ubangiji. Ina tsakar gida ina ma ƴan biyu wanka, Ummi kuma tana mana dumamen abincin kari. Uwani kuma sai gyaran ɗaki take yi ta kwanta ta hutama ranta taƙi fur. Kayan Hafizu ta jefo tsakar gidan a jaka. Ni da ummi me zamu yi in ba dariya ba. Haka Uwani ta kuma jefo kayan yaranta tsakar gidan. Wai Uwani da gaske yarannan mayar dasu zaki yi gidan Babansu, batun karatunsu a ina zai kwana. Bakya jiye musu wahalane?" "Bana jiye musu. Iyabo ke bakisan yaran da suka sha wahalar rayuwa Allah ya fi ɗaga darajarsu ba? Wallahi ko wayo da sanin ta kan duniya sunfi. Batun makaranta ba dole sai sunyi karatu zasu rayu ba. Wallahi bazan riƙe su ba gidan ubansu zasu koma" Muna cikin wannan jawabin sai ga Zaliha da yaran sun shigo. Suna ganina suka yo kaina da murnarsu. Jakar tsarabarsu na miƙa musu. "Zaliha da ke da ummi ku kwashi kayannan ku kai gidan Hafizu ku haɗa har da yaran." Mai sunan Hajiya dake itace babba tace. "Umma can zamu koma?" Uwani tace. "Canne yafi dacewa daku Ummu Kulsum. Maza bi su ummi su kaiku" Uwani ta kaɗa yarannan ko a jikinta. Harara ta doka mun ta zuba mana ɗumamen tuwonmu muka shige ciki. Saida na shirya ƴan biyu tsab na zauna muna cin abinci muna hirar yaushe gamo. Harna ba Uwani labarin naci gaba da yin makaranta kuma abun dai kamar zai ɗaure. Ki taya ni da adda'a dai Uwani. Inaso in zan tafi in yi sare_saren kayan kwalliya da magungunan mata ko da iyakar tsumi ne in jaraba. Amman meye shawararki tsoro nake ji, amman kuma zaman haka ba daɗi. Ga Hamma ni bansan ma yaushe zai dawo ba." Saida Uwani ta barbaɗa yajin daddawa ta saka lomar tuwo ta haɗiye kana tace. "Hakanma yayi Iyabo. Tunda ai dama hannu mitsiyaciyar kishiyarki ta saka miki. Yanzu kuma da izinin Allah munfi ƙarfinta. Zan kaiki gidan Sharubutu ya baki rubutu ki dinga sha. In sha Allah sai kin zama Hajiyar rugga Iyabo. In abubbuwa suka bunƙasa sai kici gaba da ɗakko kaya daga saudiyya. Ni nan da wata huɗu ma zanje saudiyyan da kaina zan saro kayan. Kinga lokacin in al'amura sun warware kasuwa ta buɗe miki sai mu tafi tare ai. In ma Hamman bai dawo ba sai ki tambayi uwar mijin naki. " Dariya nayi nace. Da wanne kudin duk za'ayi haka Uwani?" "Ke dai kiyi ta adda'a kawai. In dai Allah ya dafa miki aka ci gaba da siyan kaya a hannunki zan sai da ƙaramin gidana in ara miki jarin ki juya ki samu alkhairi. Iyabo ai hakan shine ƙawancen" Mun daɗe munata tattaunawa da ƙyar wajajen la'asar na yakice bayan na gama yima Uwani tuwon dare na leƙa gidansu Iyaa Debisi. Suna shago kamar kullum Iyaa Debisi ta hangoni, saita soma rawa tana ma ƴan biyu waƙar sunansu da yarbanci. Iyaa Kokodeen ce ta fito ita ta ɗauki Hassan Iyaa Debisi ta ɗauki Usaini. "Masha Allah yara sai girma suke yi. Ke ma ba laifi kinyi kyau ba kamar sadda muka je suna ba. Amman jibi shigarki dai irinta fulani kin ɗauko koriyar atampa kin saka" Cewar Iyaa Kokodeen kenan. Iyaa Debisi kuwa naci sa'a bata ce komai ba jikokinta sun janye mata hankali. Ina shiga gidan na tarar da Bose ta fito tana son zata tafi gida da yaranta. "Ahhh Antimi Iyabo. Kece da magriba haka muna shirin guduwa?" Rungume junanmu muka yi muna farin cikin ganin junanmu. "Ina yaran kuma?" Ta tambayeni. Suna wajen su Iyaa a waje. Na bata amsa ina Dariya. Matan gida duk suka shishshigo ganin yara bayan su Iyaa sun shigo dasu. Yaran suna da mugun farin jini sosai da sosai. Ni dai har nayi sallar isha, na fita na raka Bose da yaranta suka tafi gida. Yarannan suna hannun Iyaa Debisi. "Ina Daso, da mai gidanki, da kuma ƴan uwan naki?" Lafiya ƙalau Iyaa. Dada tace in gaisheki sosai. Ga tsarabarta nan, wannan kuma tawa ce a raba ma su Iyaa Beji." Kai Iyaa Debisi ta girgiza tace. "Angode. Iyabo kuma kina jin daɗin rayuwarki a wannan rugar? Naji labarin mijinki ya tafi cirani ya samu waiwayar gidane." Kai na sauke ƙasa a sanyaye nace. Iyaa inaji babu abinda yake damuna. Shi kuma bai dawo ba tukunna bai ko yi aike ba ma" "Hmm ba sai su shekara biyar ba ma basu waiwayi gida ba. Wasu ma sun fito sunji daɗin birni basa sake waiwayar rugarsu shinfiɗa sabuwar rayuwa suke yi. Uwani tasan kinzo kuwa?" E ta sani tama haihu jiya ta samu ɗiyarta mace. Gashi aurenta da Hafizu ma ya mutu" "Ahhh Ahhhh" Ta shiga jerawa tana dukan cinyarta. "Ai Shikenan ta huta ya huta. Ba'a matsa ma kai. Yayanki Debisi ma sun rabu da Yemisi fa. Yanzu haka yana neman wata yarinya a bayan layinnan. Kinsan gidansu Bola?" Ta tambayeni. E nasan gidansu Bola" "To yarinyar a gidan take Auwa. Yarinya mai hankali tazo ta gaisheni ma Debisin ya kawota" Allah sarki. To Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi " Tayi carab tace. "Shine ma alkhairin. Ke kinsan rikicin da akayine? Ai ni da Uwar Yemisi har abada. Yemisi fa kusan kashe Debisi tayi da duka. Duk ta farfashe mishi fuskarshi. Har ɗinki akayi mishi a gefen idanunshi. Watanshi guda a asibiti Yayanku Kokodeen na jinyarshi" Ta dinga bani labaran abubbuwan da suka faffaru, harda rashe_rashe da ƙaruwa da aka samu. Mun jima sosai kafin mu kai bacci, zuchiyata sai naji tayi sanyi sosai. Washe gari duk nabi maƙota da ƴan uwa duk aka gaggaisa. Sai wajajen azahar muka wuce gidan Uwani ni da Iyaa Debisi ta yi mata barka da jajen mutuwar aurenta ta tafi ta barni akan in anyi suna zan dawo" Mun sha suna lami lafiya. Kuma Hafizu yayi bajinta sosai, ya yanka tunkiya ƙatuwar gaske, ga kayan fitar suna kala ukku na mai jego, kala ukku na jaririyar yarinya taci sunan mahaifiyarshi. Taron suna ya watse lafiya, saina soma haramar tafiya, na shiga kasuwa na ɗan yi sare_sarena dai amman ban zura jikina ba dai Kuɗin hayane da Uwani ta ajjiyemun a wajenta da su naketa siye_siyena. Na sai su maggi, da kayan abincina harda taliyar murji Iyaa Debisi tayi mun, iyaa Kokodeen kuma ta haɗamun su elbo, da garin Amala, ga garin eba. Tsaraba dai rigijib. Uwani ma ta tsinta mun kayayyakin yara tace in siyar in jaraba ko zasu karɓu, in sun karɓu shikenan sai inci gaba da kasuwanci na. Sai da na yi sati biyu cur na tattare inawa inawa Burodami Debisi ya rakani tasha na tafi, ya bani kuɗi masu yawa, dan har nama ya kawomun mai yawa na soya nayi miyar tumaturi cikin ƙaramar robar fenti. Yanzu ya riga daya saduda yayi haƙuri har yarinyar da zai aura saida ya kawota da daddare ta gaisheni. Da yamma sakaliya sai gani na duro. Nayi lalle, da kitso, ga sabon lace da uwani ta ɗinkamun shi na sako. Matan gidan suna tsakar gidan anata hada_hadar girki sai ga ni na shigo da sallamata. Baɗɗo da Safiya ne suka tawo a guje suna yi mun oyoyo. Yaran maƙota na biye dani da kaya niƙi_niƙi. Baɗɗo ta tsaya saukesu, ni kuma na shige ɗakin Yafendo. A cikin ɗakin na tarar da Daso, da Yafendona Maman Dason kenan, da kuma Dada. "Ah Jabu kece da yamma lis haka. Lale da zuwa" Cewar Yafendo. Da fara,ata na shiga na nemi waje na zauna a gefen Daso. Sai kallona take yi, taga na sake yin kyau fiye da lokacin sunan Cubu da ta ganni, na kuma ƙiba. Damuwa to ɗaya ce a yanzu a raina rashin dawowar Yaya Hamma. Yaran na sunto a bayana idanunsu biyu na miƙa ma Yafendona ɗaya, na miƙa ma Yafendo ɗaya. Na gaishesu da ladabi. Daso ta harareni naga har yatsa sai da ta ciza. Ni dai na kada baki na gaisheta ta amsa a daƙile dai. Ni ko ko a jikina. "Kin samu su Toyosi lafiya, ya kika baro uwani?" "Lafiya lau Dada. Iyaa tace a gaisheku, su Iyaa Beji duk suna gaisheku. Uwani kuma ta samu ɗiyarta mace Fatima" "Allah ya yara, ina amsawa" Taja bakinta ta tsuke. Yafendo tace. "Hama ma ta haihu yau kwana shida kenan gobe suna. Abinda ake tattaunawa kenan ma kika shigo kika sakemu. Sai ki shirya goben aje sunan dake in Allah ya kaimu. Amman sai dai kuyi fitar sassafe ƙauyen da ɗan tafiya" Allah ya raya. Me muka samu Daso?" Na tambayeta dan itace sa'ata. Su inna tambayesu kamar nayi rashin kunyane. A taɓe tace. "Mace ta samu" To Allah ya rayata da imani. Bari inje in ɗan huta in rama sallolin da ake bina. Gaga_gaga washegari muka tashi da kacaniyar shirin zuwa suna. Ni dai har ga Allah banso ayi tafiyar dani ba gudun wulaƙanci, ga dangin Hama duk zasu ganni ƙila aita zunɗena. Kaya masu kyau sababbi fil na sama ƴan biyu. Nima na ɗakko sabuwar atampata na saka na ɗauko ɗankunne da sarƙana na saka, na saka takalmi da jaga, zobe, awarwaro duk na saka na fito shar, dama kunsan nace muku nayi kitsona, na yi ƙunshi. Sai suka sake haskani. Na goya Hassan, Safiya ta goyamun Usaini. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU (3) IYABO:. Muka haɗa kai da matan gida, da ƙawayen Hama na maƙota, da danginmu kusan mu rai ashirin, ko wacce da goyonta, wasu da yara a hannu raɓe_raɓe muka nufi gidan suna. Sai an hau keken shanu ake isa ruggar su Hama. Rugarma babu yawan bukkoki ɗan ƙaramin wajene. Tun daga nesa muke hango mata sunata shiga gidan sunannan. Da sallama muka shiga yuu. Yara na guje_gujensu manya anata hidimar gyaran kayan miya, masu tsintar shinkafa nayi. Gidan nake kallo ko da dai taro akeyi amman da gani gidan ƙazamai ne babu ko shakka. Kuma irin gidajen talakawan fulaninnan da ko akuya basu mallaka bane. Abun mamaki duk dangin Hama sun san Daso sai ambaton sunanta akeyi. Ni dai ina biye dasu har cikin wata bukka. A ciki muka tarar da Hama ɗare_ɗare a gado da jaririyarta a gefenta. Kanta an yarfa mata kitso jelarnan har gadon bayanta, ga ƙunshi tayi jawur dashi, har jaririyar akaima ƙunshin hannu da ƙafa. Akwai wasu dattijai biyu a ɗakin, da wata yarinyar mace a zaune a kan gadon da hama take. Ƙaremun kallo Hama ta shiga yi, tana kallon suturata, wani irin mugun kallo take yi mini. Hmm Waje muka samu mu mu uku muka zauna ragowar suna daga waje. Sannu mai jego, ashe kin sauka. Ina wuninku?" Na ƙarashe zancan da gaishe da matan ɗakin. Ko sun fahimci nice kishiyar Hama sai naga anyi mun amsawar wulaƙanci. Ni dai daman nasan za'a rina sai naja bakina na tsuke. Duk motsi Hama idanta na kaina. Ita bata gaisheni ba, ni dana daure na gaisheta sai tayi funfurunfus taƙi amsawa tana daga ƙwance suna magana da Daso. Baɗɗo ce ta miƙe zata ɗauko mana jaririyar ɗayar yarinyar macen dana ce muku tana zaune a bakin gado sai tayi carab ta damƙe hannun Baɗɗo" "Yarinyar bata da lafiya kar ki ma soma ɗaukarta mai son ganinta ya ganta a haka" Maganar da tsawa_tsawa da iskanci take yi. Hassanne ya soma kuka sai na suntoshi zafi na shirin kashemu. Ya haɗa zufa yayi sharkab. Duk matan ɗakin wallahi sai suka zuba ma yaronnan ido. Da naga haka saina miƙe tsaye. Zan ɗan fita daga waje in basu Mama, nan ɗin akwai zafi. Ga wannan ƴar gudunmawatace babu yawa" Na ajjiye ledar na ja hannun Baɗɗo muka fice." "Lallai saifa kin tashi tsaye. Waɗannan yaran maza kyawawa sune yaran kishiyar taki shine kike kwance kike bacci? Ai in dai da yarannan to yaranki sun zama bola a wajen Hamma" Karab a kunnena duk da dai da fullanci tayi maganar na ji tsab abinda tace ɗin. Bansan kuma wacece ba dai. Ni dai na ja turmi a tsakar gida ina shayar da biyu ina tofesu da adda'a. Yaran duk wanda ya kallesu Allah sai ya ƙara. Sabida haskensu gasu da jiki kunsan yaro mai ƙiba anfi sonshi, gasu ƴan biyu abun yayi musu yawa. Muna dai zaune su Baɗɗo sun shiga anata aiki dasu. Ni dai bansa hannuna ba kuma bazan kuwa saka ba in ji da kallon banzan ma da akeyi mini. Muna zaune da Safiya da Adda A'i yarinyar Baffa Musa muna ta hirarmu har azahar ba'a gama girki ba, har mu kai Sallah. Ni kuma yarannan gasu da tsotso yunwa ta kamani sosai. Kuma ni ko karen hauka ya cijeni ai bana sa abincin gidansu hama a bakina ba. Wallahi aka sauke abincinnan akaita rabo ni dai har abincinnan naga babu har an zuba ma tukunyar abincin ruwa. Ba'ace ku ga naku ba, amman fa iyakar mu mu ukunnan da muke zaune dan Baɗɗo dasu akai komai an zuba musu to batayi tunanin ba za'a bamu ba saita cinye abunta. Hmm sai wajajen uku na yamma aka kawo mana abincin. Shinkafa da miyace a mugun jaƙale shibkafar kamar fate, miyar kuwa yadda kukasan markaɗaɗɗiyar kabewa wai miyar stew ce. Ni dai gaskiya loma ban sa a bakina ba. Awarar nono na fita na siya naci na danne daa ruwa. A hakan ma Sai naji zuchiyata na tashi da ƙyar na mayar da aman da nake ji. Muna yin sallar la'asar muka nemi hanyar garinmu. Nasha habaici sosai. Ko wacce figaggiya sai kaji tana me za'ayi da ƙiba, ai anfi yayin mata sirara. Wata ma bata da maraba da cry fish amman sai fi'ili. Saida muka fito na sauke ajjiyar zuchiya na shaƙi iska da kyau. Washegari na tashi da kunce tsaraba da rarrabawa. Wajajen azahar na wuce gidan Dada acan muka wuni cur miyar dana tawo da'ita rabi na zabtare na kawo mata. Acan na iske Cubu da yarinyarta. Cubu wai har yanzu ashe baki koma ba?" "Bata koma ba kin ganta nan. Ni nasa an kira mun mijin nake tambayarshi ko lafiya. Yarinyarnan in laifi tayi ni ya sanar mun ya daga zuwa wankan gida zai hana yarinya komawa ɗakinta. Haƙuri dai kawai ya bamu. Ni fa jikina ya mutu gaskiya ruwa baya tsami banza" Jikina ya mutu nima. Tabbas ruwa baya tsami banza akwai wani abun a ƙasa. Kishiyoyima ai ba zasu barta ba. Amman babu komai akwai Allah. Shinkafa fara na dafa mana har dare mu ka ci Dada nama huɗu manya nasa mata da kifi, da ganda tana ci tana shi mun albarka. Ni dai tun bayan la'asar daf magriba saina soma jin wani sabon yanayi a tattare dani dai haka. A daddafe nayi Sallah ina zaune nayi tagumi sai nake jina kamar wata marar lafiya haka. Ganin ɗalibaina sun soma shigowane yasa na ɗan sake kaɗan na ƙwarara kaina. Nan muka soma karatuttukanmu bayan mun gama na baje musu kayayyaki. Allah cikin ikonshi janbaki da gazal ɗaɗɗayane kawai yayi ragowa du sun kwashe komai nerata dubu ashirin cas a cikin jakata. Bayan nayi Sallah saina goya biyu nayi ma Dada sallama muka kama hanyar gida ni dasu Baɗɗo. Ɓarayin Yafendo naje na kai mata nata shinkafa da miyar nai musu sallama na shige ɗaki na kwantar da ƴan biyu ina zaune ina harhaɗa kan kuɗaɗen ciniki, da kuɗaɗen da nazo dasu, da wanda Burodami Debisi ya bani. Sai naji gabana yayi mummunar faɗuwa. Ba shiri na dafe ƙirjina na runtse idanuna. Daga haka sai nayi maza na miƙe tsaye na cusa kuɗaɗennan a jaka. Na saɓa biyu a bayana, na mayar da mayafina na suri ƙaramar jakar da kuɗina ke ciki. Wallahi tiryan_tiryan ba saina fice a gidanba na naushi hanya, inayi ina haɗawa da gudu_gudu. A lokacin wata guguwace nake jin tana tashi a kaina, ji nake kamar zan rasa rayuwata inna ci gaba da shaƙar iskar Jaɓɓi lamba. Hakanne yasa na shiga gudu_gudu burina in bar rugar kawai. Babu wani tunani a kaina, bana iya tunanin komai burina na barin garinne. Ina fitowa kan iyaka na samu mota ta cika zata Girai saina faɗa motarnan. Ina zaune shiru kaina na wani irin zafi da ciwo. Gaga_gaga muka iso Girei. Na kuma samun motar cikin gari nanma na shige. Banfa san ina zanje ba, ni dai burina inyi nisa kawai. Muna shigowa tasha aka saukemu. Nayi tsayuwata a gefe nayi shiru. Nafi minti sama da talatin a wajen. Wani ɗan wuniyonne yace. Hajiya ga rumfa can da ƴan uwanki mata kije ki zauna mana. Hala kema fasinjar Lagos ɗince? Gashi motar ce ta samu matsala tashi sai gobe da sassafe. Ko kin fita ba zaki samu abun hawa ba" Haka nabi bayan bawan Allahnnan izuwa rumfar da matannan suke. Harda masu goyo. Waje na samu na zauna shiru. Hankalina baya jikina bansan meke mun daɗi ba sam. Amman nasan nice Iyabo, Hassan da Usaini Ƴaƴanane iyakar abinda kaɗai nake tunawa kenan fa, duk rayuwata da asalina ya goge a kaina bansan kowa ba sai kaina da ƴaƴana fa. Allah gwanin iko da hikima. Allah ya tsare duk mata da sharrin kishiya mai asiri. Gata ayi fito na fito, ko makirci ko kuita cin uwar sabada a tsakar gida. Duk macen da aka taɓa yima asirin gusar da hankali da tunanine kaɗai zasu fahimci Iyabo. Gaga_gaga cikin dare kowa yayi bacci, ammanni ina zaune na zuba ma yarana dake bacci saman cinyoyina idanu ina kukan da bansan dalilin yinshi ba. Sai in dinga jin kamar ana kiran sunana. Wannan dare shine dare mafi muni a rayuwata. Sauƙin dana samu asussuba muna idar da Sallah akace mu shiga mota. Ni dai matan da muka kwana rumfa ɗaya nabi muka shiga wata ƙatuwar mota muka zazzauna mazanmu da matanmu dukka. Kuɗin mota akace mun biya nera dubu biyar. Na ƙirga na bayar. Matar dake kusa da kujerata na tambaya. Dan Allah baiwar Allah motar inace wannan wanne garin zata je?" "Lagos zata je ke ɗin bakisan motar ina kika shiga ba har kika biya kuɗi?" A_a ba haka bane" Iyakar abinda nace kenan. Idanuna na lumshe na dinga hawaye. Motarmu ta fice a tasharnan duku_duku muka kama hanya, tafiya muke yi, muna wuce ƙauyuka, da garuruwa. Mune har azahar muna tafiya sai lokacin na ji zuchiyata tana ɗan rage nauyi da sanyi haka. Da muka shiga wani gidan mai inda zamu yi sallah muci abincine ma sai naji inajin yinwa musamman da naga balangu, da zire, da abinci anata siye. Sallar na soma yi, sai na sai tuwon sakwara da miyar egusi, da ruwa na koma mota. Kari ɗaya naci tuwon ɗayan kar n na ba ƴan biyu suka ci suka sha ruwa. Nabkin ɗin jikinsu ya jiƙe sharkab. Sake fita nayi na sayi ruwa na cire musu nabkin ɗin na wanke musu kashi, na ƙulle tsummokaran a leda a wajen na barshi. Ina shiga motar direba ya tashi mota dama ni ake jira. Ɗankwalin kayana na zare na keta shi biyu dashi nayi musu sabon ƙunzugu. Gaga_gaga mukaita tafiya kiki_kiki mune la'asar magriba, isha. Ni dai ina zaune ina kallon titi wani irin sanyin ni'ima da kwanciyar hankali na saukarmun wanda bai da tamka. Yarana na kalla suna cinyata suna wasansu. Murmushi nayi na shafi kansu, bana iya tuno kowa da komai, yarannan dake cinyata su kaɗai na sani abun mamaki ko? Wallahi babu mamaki a duniyarnan babu abinda ba'ayi sai in bai zo kan ka ba ko kan wani naka ba shine zaka yi mamaki, ko kan ka yaƙi ɗauka ma. Misalin ƙarfe taran dare motarmu ta shiga gareji mun iso cikin yardar Ubangiji. Duk muka sakko ƙafafuwanmu a kumbure. Ni dai babu wanda na sani bansan inda zan nufa ba. Titi kawai naje na tsaya inata kallon motoci suna wucewa. Lagos gidan cunkoso kenan. Motoci iri iri sukaita wucewa, ga jama'a a ƙafa sai yawo suke yi. Da dai naga wankin hula yana shirin kaini dare saina koma cikin tashar na shiga rumfar wata bahaushiya mai saida masa da tuwo na zauna. Wata matar shagon ta iso inda nake tace. "Tuwo ko masa kike buƙata?" Masa zaki zuba mun. Amman kafinnan dan girman Allah ku taimaka mun da masauki ni baƙuwace bansan kowa ba a garinnan" Kallona tayi da kyau ta dubi yaran hannuna tace. "Amman baiwar Allah da yarannan kika shigo bariki maimakon ki barsu a gidan ubansu. Nasan bazai wuce takaicin rijalu bane ya sa kika fito yawon duniya ba. Zan kawo miki tuwo in mun tashi zan haɗaki da Hajiya mai shagonnan ƙila ta taimaka miki da masauki amman bafa kyauta ba. Nan Lagos kika shigo kowa kika gani a nan kuɗi ya fito biɗa. Masar nawa zan sa miki?" Nera ɗari uku na bata ta wuce bata jima ba ta kawo mun masar. Hassan na sunto na soma ba, daya ƙoshi na ba Usaini ma kafin na ci nima muka sha ruwa na takure a gefe. Jama'a sukaita shigowa wannan shago. Dare yanata tsalawa. Wannan dai mata itace ta zo inda nake tace. "Baiwar Allah kizo muje office Hajiya ta ganki." Miƙewa nayi da saurina nabi bayanta. Ma'aikata sai miƙa ma mutane abinci suke yi. Ga ƴan mata tsula_tsula cikin kwalliya suna tafe da yanga. Matanma kamar zaɓarsu akeyi ko wacce babu muni a tattare da'ita. Cikin ofishinnan muka shiga. Wata shirgegiyar Hajiya kamar ni tana zaune ga kuɗi cikin robar fenti babba a gabanta sai haɗasu take yi. Ga wasu bandir_bandir a gefenta ta haɗa. Taci uwar bilicin, ga kwalliya ta alfarma sai cin cingam take yi" "Hauwa wannan ce matar da kike faɗamun, yo baiwar Allah zaki fito bariki da yara har biyu keko taya zaki samu aiki? A_a wallahi ni bazan iyaba. Kuma kinyi ƙiba da yawa ma'aikatana kinga ƴan madaidaitane masu jawo hankalin maza dai." Ni dai nayi shiru ina saurarenta. Wacce ta kira Hauwa tace. "Hajja Mama a duba na fahimci kamar gudowa tayi, dan ko jaka bata riƙo ba na kaya. A duba dai" Da harara matar ta bini. "Menene sunanki, kuma daga wanne garin kike?" Sunana Iyabo Hajiya. Bansan daga wanne garin nima nake ba, amman dai garinmu da nisa gaskiya " "To dake dai naji kince sunanki Iyabo. Ke beyerabiya ce, ku yarbawa an sanku da juriyar aiki. Zan taimaka miki zan tafi dake gidana zaki zauna a hannuna. Amman duk sati zaki biya nera dubu biyu kuɗin ɗaki, kullum ɗari biyu ake biya. Ina bayar da abinci wannan ba matsala bane tunda kune masu aikin abincin. Zan duba inga a wanne gurbi zan saki. Sai dai inada sharaɗi in kinsan yaranki masu kukane to wallahi kona ɗaukeki zan sallamekine ehe. Bazai yiwu na rufe shago biyun dare ba inaso inje in huta ace kuma yara sun hanani bacci ba" Jikina na rawa na dinga jero mata godiya harda tsugunnawa. A ofishin na rama sallolin da duk ake bina. Na zauna a gefe Hajiyannan sai kuɗi take ƙirgawa, Hauwa na sake juyo mata kuɗin daga ƙaramar robar fenti. Yadda tsarin ofishin yake, wata ƴar ƙoface kamar taga amman ta gilashi. Anan masu siyen abinci suke biyan kuɗin abincin, sai suje su zauna a tura yara su kai musu abincin. Hajiya kuma tana Hakimce tana tattare kan kuɗaɗenta. Wayarta ce tai ƙara ta duba tana ƙirga kuɗi. "To yau kuma an tuno dani kenan Dr manya" Wayar ta ɗauka tace. "Likita bokan turai kaddai ka shigo Lagos ne yasa ka kirani? Dan na fahimci abincin Hajja kaɗai kake son ci, da zaran ka bar Lagos kiran waya ya ƙare" Na cikin wayar bana jin abinda yake cewa. Jim tayi dai tana saurarenshi kafin ta ɗaura da cewa" "Ai in akwatin aure kake so ka samu balle akwatin me jego. Kai dai turo kuɗi kawai Alhaji za'a haɗama akwatin kayan fitar suna. Ina da tela duka ɗauka wannan wanda ya taɓa ma Amaryarka ɗinkin kayan lefe? To shi in harda dinkin ma za'ayi maka duka" Sai ta kuma tin jim. "To to Shikenan Alh sai na ji Alart sai kuma ka faɗamun wacce kala uwargidan tafi so. Sabida asai mata kayan da zai ƙayatar da'ita. Sai na jika likita bokan turai" Ta ajjiye wayar tana dariya tana ƙirga kuɗi abunta. Muna wannan shago har biyun dare masa dai ta ƙare tas tuwonne ma akwai ragowa. Nan aka shiga hada_hadar tattare kayayyakin daya dace. Akayi wanke_wanke da gyaran wajen tas. To a gaskiya zagewa nayi na tayasu aiki. Saina fahimci kazarniyata ta burge Hajja dama ni fatana kenan. Muka kama hanyar gida da wata akwalar motar hajja. Kusan mu rai goma a mota ɗaya gashi ni ba kaɗan ba ga yara a bayana. Sai sakkosu nayi aka riƙe mun su na saka ƴan mata biyu a cinyata suka zauna. Munyi tafiya mai nisa kafin muka shigo wata unguwa. Abun mamaki sai nake ganin mutane a layin kamar ma ba tsakiyar dare ba. Ga masu siyar da abinci nono_nono a jejjere. Ga kuma mutane a titi suna baccinsu, wasu a ƙofar masallaci, wasu akan teburan masu kayan miya. A wani gida da akayi mishi katangar kwano muka tsaya duk muka sassauko. Ni dai biye dasu nake har cikin gidan. Hmmmm fasalta ƙazantar dake cikin wannan gida ɓata lokacine, masu saurin amai da tashin zuchiya sai suyi. Haka dai muka shiga wani ɗaki ɗan ƙub ciki da falo. Ɗakin duk shirgi, ga mata har guda biyar a kwance, banda waɗanda muka tsallake muka shiga. "Ke Iyabo. Ku raɓa ta can lungun kujerar zaki ɗanfi samun sakewa kar a tumurmushe miki yaranki, naga ma basu da rigima sai baccinsu suke yi." Cewar Hajja Mama kenan. Inda ta nunamun na wuce da yarana. A tantagaryar ƙasa na kwanta, na shinfiɗa mayafina na shinfiɗe yaran. Nayi shiru inata kallon sama kawai, so nake inyi tunani akan wani abu ko guda ɗayane, amman koma nace zanyi iyakar abinda nake tunowa hanyar motane kawai inna matsa sai ciwon kai da tashin hankali kuma.Idanu na lumshe na shiga kallon matan dake cuccure a waje guda, sai tusa suke sakewa ɗaki ya cika da wari, ga masu gwarti sai ja da sakewa suke yi. Banci ya ɗaukeni baifi da minti goma ba akayi kiran assatu a masallaci. Kowa saiya tashi. Kafin sallah gidannan ya karaɗe da hacaniya sai girke_girke akeyi matan gidan na abincin saidawa. Hajja Mama ma tuni ta ba da oda an gangama tukwanen girki, ni kuma muna ta wanke farar shinkafar masa ni da wata mata dan zata yini a shekaru" "Jiya kika zo garinne baiwar Allah. Na ganki da yara kuma. Ai yawon bariki ba'a fitowa da yara. Ko gudowa zaki yi ba sai ki bar yaran a wajen ubansu ba. Nifa yarana bakwai haka na tsallako na barsu kuma ni da komawa ganinsu saidai a darussalami" Na dubeta nace. Jiya nazo, yara bani da inda zan ajjiyesune." "Sai dai zasu iya hanaki yin aikinki yadda ya kamata. Koma naga kina da ƙwazo. Sunana Batula kefa?" Iyabo sunana." Muna dai aikinnan tana taɓomin hira haka, dake Batula irin matannanne masu saurin sakewa masu fasa cikinsu ga kowa. Muna gamawa aka tashi injin niƙa. Ni na niƙa shinkafar masarnan nayi mata niƙan daya kamata. Aka saka kanwa da gishiri aka rurrufe. Sannan fa lokacin sallah yayi, masu yin Sallah muka je muka yo, muka dawo, waɗanda suke fashi suka ci gaba da aikinsu. Ina idar da sallah ƴan biyu suka tashi, wata budurwa dake zaune gama wayarta kenan tace. "Wannan yaran ba dai kyau ba gaskiya, gashi sunyi kama sosai" murmushi nayi mata nayi godiya na saɓesu muka fito . Hauwa inason zansai tawul ɗin nabkin ne, yarannan kafin su tsuleni da fitsari." Hauwa ta ɗago tace. "Kawo kuɗin aba yarinya ta karɓo miki" Kuɗin na koma naje na dakko" "Ɗauko kuɗinki ki ɗaureshi a mararki kafin kiji wayam wallahi. Ba'a ajjiye kuɗi sakaka, wallahi har a jikinki sai a lalubeki kina baccin asara a yashe kuɗaɗen. Iyami zo ki karɓo mana famfas maza" Wata yarinyace a guje tazo ta karɓi kuɗin ta tafi. Hauwa ta kaɗa kai tace. "Kin ganta ƴar gaba da fatiha ce, muna zaune uwar tayo cikinta ta haifeta gashi muna morarta" Idanu na zaro zanyi magana ta rufe mun baki da hannunta. "Kije ki kama aiki, ki tambayo Hajja Mama me zakiyi" A wajenta na bar biyu naje na sameta a hakimce tana shan tea da biredi da wainar ƙwai. Hajja Mama mai zanyi kuma?" Saida ta gama mulki tace. "Za'a soma sallamar siyan tuwo ɗumame. Kunu zaku dama ke da Batula ku sassallami masu cin tuwo. Da rana a gidannan anayin ɗanwake. Dake da Rabi'a, da Samira, da Batula, da waccan tsohuwar karuwar zaku dinga yi. Dama suna ƙorafin aikin yana ɗan musu yawa sai ki kama musu. Bazan iya fita dake shagona da yara ba, aikin ki zai zama na gidane kawai. A wata kuɗinki nera dubu goma, kullum kuma kuɗin wajen kwanciya ɗari biyu, in kuma wata zaki biya dubu biyu. Abinci sai kin ture. Ba'aimun wasa da kasuwancina. Bazan hanaki yawonki ko kula maza, ko karuwai ba. Amman a tabbatar an gamamun kasuwancina tsab tukunna. Banda ɗauko cikin shege kuma na gaji da ƴan dakan kuka a cikin gidannan. Iya wannan shine sharaɗina, da zaran kun dama kunu kusha kuci tuwo ku ƙoshi ku samu ƙarfin yin aiki. Hauwa zata fito tuyar masa." Nagode sosai Hajiya, Allah ya sa ma kuɗin albarka." Daga haka na fito muka shiga aiki bayan munci mun ƙoshi. Ƴan biyu sunata jan ciki a tsakar gidan suna wasansu mu kuma munata aikin sakun ɗanwake, su Hauwa suna tuyar masa. Sai da akayi azahar Hajja Mama ta fice da tawagarta zuwa shago. Ni kuma naje nayo Sallah na dawo muka ci gaba da sallamar masu siyan ɗanwake. Abinda na lura salla bata damesu ba a gidan neman kuɗin kawai suka saka a gabansu. "Iyabo ga abincin ranarki ke da yaran" Batula ta miƙo mun ɗanwake yaji mai da yaji, yayi daɗi sosai kuwa, gashi ishasshe. Gaga_gaga bamu muka kammala saida ɗanwake ba sai bayan la'asar masu wanke_wanke suka kama aikinsu, mu kuma muka gyare wajen tsab ko wacce tayi wanka suka soma ficewa. Kafin magriba ɗakinmu daga ni sai Baba. Wata babbar matace, tana zaune tanata harhaɗa kuɗin ciniki. "Kina ta gani ana watsewa ko? Sun tafi yawon ɓelɓel yawon raba jiki ma mazan bariki. To rayuwace ta ƴancin kai babu makwaɓi. Nima a shekarun baya babu abinda ni banyi ba. Dan nafi shekara ashirin a garinnan. Silar auren dole ce tasa na tsallake iyayena na shigo Lagos da ƙunshin kayana a ɗankwali. mun dama duniya da dukiya, munyi cuɗanya da mutane manya sosai. Sau biyu inayin aure a garinnan zamanne yaƙi daɗi, gashi ni kuma na saba da riƙe kuɗi sai kawai kiga nayi fitowata. Amman ina baki shawara yadda kika kwaso ƴaƴa haka karki sake kice zaki yi zaman karuwanci da yara a gabanki. Kinga ɗakunan dake jere uku ta hagun ɗakinnan? Duk ɗakin yaran mata irinkine daduro sun ajjiyesu suna musu komai tamkar aurensu suka yi. Kuma fa su suna da matansu a arewa amman kuɗinsu akan waɗannan kilakan yake ƙarewa sune komai nasu. In aure mace take so ta samo miji Hajja Mama na tsaya mata ayi bikin sumul ba tare da iyayenta ma sun sani ba. Tsuru_tsuru nayi ina sauraren abun al'ajabi. Mun jima sosai tana koramin bayanin yadda ake rayuwa a Lagos. Ni dai anayin isha ni da yaran mu ka yi baccinmu harda minshari sai da duku_duku muka sake tashi da aiki. Ni da Batula kamar jiya mukaita aikin siyarma da ƴan cirani ɗumamen tuwonnan. Ga masa daga gefe Hauwa na toyawa. A cikin gidan fa akwai masu abincin siyarwa sosai, kuma ko wacce mai abinci da ma'aikatanta. Hakanne yasa gidan kullum a jaƙale ko ina ruwa, ga tulin wanke_wanke, wanda akasari mazane ake biyansu su dinga yi. "Iyabo goma fa tayi ki daure ki zauna kici abincinku kafin mu ɗaura tukunyar ɗanwake kuma. Sai munje kasuwa mu siyo yaji, yau bamu da yaji da mai. Kayan Hajja Mama basu iso daga Arewa ba. Kunji sabon halin da Iyabo ta tsinci kanta kuma a ciki ko? Kar dai ku mance wannan labarin ba ƙirƙirarre bane labarine daya faru a gasken_gaske. Anayin asirin da yafi wannan muni, tunda ana haukata mutum, a kashe mutum, ko ayi ma mace kurciya kamar yadda akayi ma Iyabo. Wasu ko sunansu basa iya tunawa ma. Allah ya rabamu da aikata aikin dana sani Mata aji tsoron Allah kar kije ki tura kanki layin ƴan wuta. Shi rijalu da kike yi dominshi ki ganshi a layin ƴan aljanna kinga kinzo duniya a banza kin koma a hofi akan kishin banza da wofi. Da anyi magana acd ciwon ƴa mace na ƴa mace ne. Ko wacce ƴa macen ake nufi oho. Post ya monday in sha Allah. Ban rufe ku.ba idanuna ke ciwo dan Allah masu ƙorafi ku yi mun uziri ai ya kamata ku shaideni in dai posting akan kari ne da redmore in ba'a yabeni ba ba a zageni ba. Lafiya fa uwar jiki balle idanu ba'a wasa dashi. Nagode sai mun haɗe MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU... ROMO ƊAÑYE LITTAFI NA HUƊU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI (4) GWADABE:. "Me ya faru Bara'u. Wani abunne ya samu Babala kuma, amman naji kana cewa duk gari anata tsogumi?" Gwadabe yayi kasaƙe yana sauraren abinda Bara'u zaice mishi. "Laila ai ba ƙaramar matsiyaciya bace Gwadabe Allah ne kaɗai ya taimakeka ka kubce ma auren Laila fa" Gwadabe yayi dariya yace. "Yauwa nasan za'a runa ai wai an saci zanin mahaukaciya. Ta yashe Yaya Hambalin ko?" Bara'u yace. "Abun ya wuce tunaninka. Asiri tayi ta mallake Hambali Gwadabe. Laila ta dinga mulki tana iskanci. Kaga dai kab su Fudiyo Laila tasa Yaya Hambali ya koresu daga gidanshi. To sai suka garzayo suka sanarma Babala. Batai ƙasa a guiwa ba tasa su Da'u a gaba suka je Kano. Laila ta zage taci mutuncin Babala kuma tasa Yaya Hambali ya koreta ta dawo Takai. Kaji wannan? Bai tsaya iya nan ba Gwadabe tasa Yaya Hambali ya dinga ɓarnatar mata da dukiyarshi ita da Baba Iyatu. Ya dena zuwa Takai, ya dena turoma Babala abinci. Su Da'u su ba jari ba dan tasa an ƙwace komai a hannunsu. Su sun ajjiye matan anan cikin gidanku, su kuma sun bazama neman na kai. Wannan dalilinne ya kwantar da Babala a asibiti. Kai Gwadabe yaita girgizawa yana mamakin wannan lamarin" "Haula da yaranta fa su kuma?" "Wacece wata Haula anaima batun Babala? Ai ya daɗe da rabuwa da Haula, yaran dai marasa auren suna hannun ita Lailan tana gasa musu aya a hannu. Kasan dama ba mutunci bane dasu suna, Layla na koya musu hankali. Wai kai kaga Yaya Hambali yadda ya koma kafin tace? Abun yayi baƙin muni gaskiya rashin imanin yayi yawa. Gwadabe rikici fa da Babala da Baba Iyatu har gaban mai gari. Baba iyatu tayi butulci sosai bata kyauta ma Babala ba gaskiya. Duk da dai bayan faruwar abun Takai ta ɗauka duk inda ka wuce labarin akeyi. Nifa ji nayi ana cewa bata hanyar halak Yaya Hambali ya samu arziki da ɗaukakar ba, wai yana bin ƴan bori. Wallahi ance wai shima har borin yake hawa. Wannan kwalli da yake dumbuzawa a idon shi bafa na lafiya bane ashe. Kai maganganu iri da kala anata rarrabawa a Takai wallahi. Babala ko fitowa bata iyayi sabida kunya. Yaya Halima ma ta ƙare mata reshe ya juye da mujiya kishiyarta ta mallaketa sai yadda tayi da'ita. A wata ruwayar ma cewa akayi Yaya Halima har wanki take ma kishiyar tata." Ajjiyar zuchiya ya sauke yace. "To Allah ya kiyaye gaba yasa wannan abun daya faru Babala ta sassautamun, ta gane dalilin da yasa naƙi auren Laila" Bara'u ya dafa Gwadabe yace. "Hmm kullum fa a sunturin bin ƙauyuka suke suma suna neman ai musu asirin da Hambali zai rabu da Laila hankalinshi kuma ya dawo jikinshi. Sannan a karya asirin da Kishiyar Yaya Halima tayi mata. Yaya Halima ta manta a shekarun baya har zane kishiyarta take yi, meye batai mata ba? Wanzami baison jarfa. Yanzu labarinnan da nake yi maka da Laila da Baba Iyatu fa suna Umara. Shi kuma Yaya Hambali an yi mishi kiran duniya dan ma a sanar mishi da halin da Babala take ciki, wallahi yaƙi ɗaga wayar fur. Aka tashi Da'u yaje Kanon ma ya kasa ganin Hambalin sam. Jiya saini da naje ne na biya musu kuɗin maganin da aka rubutama ita Babalan. To babu kuɗin komanta ya ƙare har gonarta ta siyar danta dawo da tunanin Hambali amman ina. Tai ta kuka a asibitinnan in faɗa maka. Ina asibitin ban tafi ba Yaya Halima take bata labarin an mata kwatancen wani boka zata je wai ko Allah zaisa a dace. Sai dai basu da kuɗi komansu ya ƙare. A haka dai nayi musu sallama na tafi. Ya suka ƙare oho" Shiru Gwadabe yayi yana mamakin wannan lamari. Sai yaji tausayin Babala ya kamashi abunka da uwa. Hatta su Da'u ya tausaya musu sosai. "Zan ajjiye maka ishasshen kuɗi dan Allah ka kula da komai nata. Kada ka sake kace mata nine. Abincinma zan dinga aiko maka da kuɗin duk wata a dinga siya mata" Motar Zulƙi ce tazo wucewa ganin su Bara'u ne yasa ya tsaya. Tashi suka yi suka nufeshi. "Kaga mai maganin harka Gwadabe mai maganin ɗa'a ashe kai ka shigo garin ma shine babu labari? Nama kira wayarka har sau biyu baka ɗaga ba dan akwai magana ta ƙaruwa gaskiya " Hannu Gwadabe ya bashi suka tafa sunata dariya. "Baka da dama wallahi Zulƙe." "Ai gaskiya ne. Uwargida tana ta yaba canjin da aka samu. Duk manyan mutanen dana haɗaka fa dasu sunata son magani na ba wasu numbarka jiya dan mun yi meeting ne shigowata garin kenan. Gashi dama ko bamu haɗu ba na kiraka a waya dan mu tattauna muhimmiyar magana ne." Gwadabe yace. "Bazai gagaraba. Zuwa gobe da safe zamu shigo kaga maci masa ma mu more. Nima ko awa ɗaya banyi da shigowa garin ba" "To Shikenan hakanma yayi. Bara'u sai kun shigo zan jiraku" Nan su kai sallama, Gwadabe ya samu ya shiga wajen Sakina suna cikin ɗaki suna zazzaune. Hadiza na gefe guda a takure tana cin tuwo. Shafa ma tana nata gefen tana cin nata tuwon. Sakina kuma tana bama jaririyarta nono, sai yara daketa shirmensu dai. Suna ganin Gwadabe suka isa a guje da oyoyo. Tsugunnawa yayi duk suka dafashi ya kalli Toye da su Kahinde yaga yadda suka yi baƙi suka rame, ga ƙuraje bajaja a jikinsu. Kai ya girgiza kawai yana jimantawa Iyabo. "A_a kaga Tsuntsun soyayya maraba da zuwanku. Sai yanzu ka shigo, Bara'u baka shigo dashi yaci tuwon ba" Bara'u yace. "Wanne tuwo ana zaune lafiya. Bari a karɓo kaza mana, ki haɗa musu tea kafin mu dawo. Kaga tsuntsun soyayya kake ko? Tawo muje" Da Sakina da Shafa sunata musu dariya. Hadiza kuwa ta mugun takure kanta. Ko dariyar ma ta kasa yi. Duk yadda Sakina taso tasa Hadiza ta sake amman taƙi fur. A hanyar dawowarsu daga siyo kazane Bara'u ya shiga ba Gwadabe labarin Iyabo. "Kai in kaga irin ƙauyen da tsuntsun soyayya take rayuwa in dai kai kaje nasan ba zaka iya bacci ba Gwadabe. Nifa kaina ranar kasa bacci nayi inata tubkewa da warwarewa. Amman shi sha'anin aure ƙaddarane zallah a cikinshi. Gashi ta haifi yaranta ƴan biyu kyawawa baka gansu ba. Mijin ma baya nan ya tafi kiwon shanu. Amman taji daɗin saƙon dana kai mata nace in jika tayi murmushi ta karɓa tayi godiya. Yaran dana koma ɗakkosu tayi musu tsaraba sosai harda matanka taima tsaraba kuma tace ai musu ma godiya bisa riƙon yara da suke yi. Ni dai lamarin ya dameni gaskiya " Murmmusawa Gwadabe yayi yana goye da hannayenshi a bayanshi yace. "Soyayya ce nayi imanin yake riƙe da Iyabo a wannan Rugga nayi imanin hakan. Nasan Iyabo sama da sanin da taima kanta ita kanta. Fatana shine Allah yasa mijinta yana riƙeta da kyau dan ya more mace, ba fishi, ba ƙorafi, ba hayaniya, ba rainuwa, ita dai kamar ba jinin yarbawaba. Gashi dangin mahaifinta mugayen jarababbune. Allah sarki Iyabo tsuntsun soyayya ƴar a mutu ma soyayya kenan." Dariya Bara'u yayi yace. "Taga ɗan fulani siriri mai siririn hanci fari mai gashi a kwance, ba irin naka gashin duk ƙuda ba" Naushi Gwadabe ya kaima Bara'u yayi saurin kaucewa ya naushi iska. Har suka shiga gida Bara'u na ma Gwadabe dariyar mugunta. Shiko ya mugun haɗe ranshi sai tura tumbinshi yake yi. Kajinnan Sakina ta raba, ta cira ma yara nasu harma sunyi baccinsu ajjiye musu tayi da safe saci. Ta cirama Gwadabe da matanshi, ta cire nata da mijinta. Suna cin kaza suna hirarsu. Sakina ta shiga ciki ta ɗebo tsarabar da Iyabo taima yara ta dure a gaban Gwadabe. "Ga kayannan Gwadabe gara dai ku gani sai kaba matanka su adana a jakarsu, gidan gobe zai haɗa jama'a." Hadiza ta dubi kayan ta haɗiye tsokar da tasa a bakinta ba bare data tauna ba dan baƙin ciki. Bara'u yace. "Wannan atampopin na matanka ne tace a basu. Wannan kuma na yaranne, wannan tace a ɗinka ma takwararta, a goyata dashi. Taji daɗin ganin hoton takwararta fiye da yanda kakr tunani. Taba Sakina nata daban. Nono dai mun shanye, amman akwai soyayyen man shanu da yawa naku na ajjiye. Kaji, ko zabuwane nasa anyi mana miya mun cinye" Gwadabe yayi shiru kome yake tunani oho. Can ya nisa yace. "Allah ya saka mata da mafificin alkhairi. Ku kunji ga fa kaya Iyabo ta aiko muku dashi." Ya dubesu yana karantar yanayinsu. Shafa cikin fara,a tace. "Mungode Allah ya saka da Alkhairi . Takwararta tana godiya. A gaskiya Mamansu Toye tana da kirki da sanin mutuncin mutane. Dole ma ta tsaya aran uban ƴaƴanta gaskiya. Mu bamu iya bata tsarababa ita ta aiko mana dashi. Madallah da Iyabo mutuniyar kirki" Gwadabe take yaji matsayi da soyayyar Shafa ta nunku a zuchiyarshi. Idanu ya lumshe kawai baice komai ba. Hadiza dai sai cin kazarta take yi ko tari batai ba. Bara'u daya lura da hakan sai ya soko ma Gwadabe batun noma" Gwadabe yaba matanshi umarnin bama Sakina gudunmawarsu tun yanzu dan da safe kacamewa gidan zaiyi da mata. Sakina tayi godiya sosai. Nan suka tashi tare dayi musu sallama a ɗakin zaure suka kwana. Gwadabe da ƙyar bacci ya sureshi. Damuwar Iyabo ta addabeshi. Da kuma tunanin irin rashin kyautawar Laila ga Babala duk irin soyayyar da Babala ta nuna mata ita da mahaifiyarta sakamakonta a wajensu kenan? Wani ɓangare na zuchiyarshi yace dashi. "Tsuntsun da yaja ruwa ai shi ruwa kan doka. Ba dai ita take son rufama Laila asiri ba. Ita gashi ta bankaɗa asirinta ai" Da waɗannan tunane_tunanen bacci ya ɗebeshi" Washegari . Aka wayi gari da hada_hadar suna. Mata na ciki suna hidima, su Bara'u na waje suna kiciniyar yanka tunkiyar suna. Ƙanin Bara'u suka bari da ragowar aiki suka nufi gidan Zulƙi dan dukkansu a matse suke da son jin menene Zulƙi yake son ya tattauna da Gwadabe. A falon baƙi suka yada zanzo, aka cika musu gabansu da kayan ciye_ciye da kayan tea. Yau Zulƙi bai ɗauki lokaci ba sai gashi ya fito daga ciki da ƴarshi ƙarama a kafaɗarshi mai shan Nono" "Gwadabe mai maganin harka. An gaisheka likitan maza" Bara'u ya durƙusa ya dinga sheƙa dariya. Da Gwadabe da Zulƙi ma dariyar suketa ɓaɓɓakawa da ƙyar dariyar ta lafa aka ɗaura da gaishe_,gaishe. "Ya kujerar muƙami ya akaji da jama'a kuma?" "Gwadabe ga kujera nan lokaci ya kusan cin mana. Dama akan abinda nake son muyi magana kenan. So nake yi a zaɓe na gaba mu tsayar da kai a matsayin ɗan takararmu Gwadabe. Nasan wallahi zaka iya shi yasa da muka yi taron meeting Chairman na Takai ya bani umarnin in akwai wanda nake ganin ya cancanta to in kawoshi ni da kaina. Ni kuma duk hange_hangena a cikin abokanmu kai kaɗai na hango sabida kaine kake da takaddar shaidar sakandare. Amincewarka nake nema sai kuma in ɗaukeka in kaika wajen Chairman ku gana. A ɗaukeka a tsomaka a party" Tunda Zulƙi ya soma magana zufa ta soma karyoma Gwadabe. Bara'u kuwa sai washe baki na farin ciki yake yi. Wata ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke kana yace. "Bazan iya siyasa ba balle har in riƙe wani muƙami ba Zulƙi. A nemi wani a saka ni sana'ata ta fiye mun komai. Ina tsoron danne hakkin al'ummar data rataya bisa wuyana. Gidana ma ban gama bi dasu ba wallahi. Mata in suka haɗa maka tenshon sai kaji kamar kayi musu ƙaura, ina ga jagorancin al'umma?" Da Bara'u da Zulƙi suka haɗe bakunansu wajen cewa. "Zaka iya kujerar dakai tafi dacewa" Dariya suka yi duka. Zulƙi yace. "Gwadabe kar ka buɗamun ƙasa a idanuna mana. Ka daure mufa amincewarka kawai muke buƙata, ba'a buƙatar ko sisinka yardarka kawai ake nema. Kuma ka sani ai zaɓe za'ayi matawar jama'ar gundumarka suka zaɓeka to tabbas ka cancanta. Gidanku babban gidane kuma sananne, nima naci zaɓe balle kai Gwadabe. Ni da Alkhairi na soka Bara'u ya bani labarin duk halin da kake ciki da danginka da Babala. Har asibiti ma naje na dubata." Zulƙi da Bara'u sukaita ba Gwadabe baki, shi kuma yana nuna musu girman jagorancin al'umma. "To naji na amince Allah yasa hanyar arzikin kenan. Amman zan zauna da matana muyi shawara ko ba gaskiya bane?" Zulƙi yace. "Wannan gaskiya ne. Amman shawarar karya wuce yau. Tunda dai gaka a Takai sai muyi komai mu gama mu san mun samu cansila mai jiran kujera" Dariya su ka yi dukansu. "To Alhamdulillah Zulƙi kayi zumunci. Gwadabe ka kyauta daka amshi wannan tayin. Kuma ayi istikara Allah yasa albarka a cikin lamarin. Muyi ta adda'a, mu kuma zamu shiga mu fita da izinin zaka samu wannan kujerar." Murmushi Gwadabe yayi kawai. Wayarshi ce tayi ruri. Ya ciro a aljihunshi ya kara a kunnenshi. "Alhaji barka da safiya, kaine da waya sassafe haka?" Alhajin yace. "Dole in kiraka. Na jima ina neman maganin lalurata ban samu ba. Amman cikin yardar Ubangiji sha biyu nayi ma maganinka na samu waraka. Sabida wannan na biya maka umara da kai da matarka in sha Allah. Wannan shine tukuicina na jin daɗin maganinnan." Kabbara Gwadabe yayi harda miƙewa tsaye dan murna. Nan ya dinga ragargazo mishi godiya. Da haka su kai sallama ya ajjiye wayar. "Ku taya ni murna wannan babban mai muƙamine na bashi magani ya samu waraka shine ya biya mana kujerar umara" "Allahu Akbar. Allah da girma yake haƙiƙa na taya ka murnar wannan tukuicin Gwadabe. Allah yasa shekarar arzikinka da ɗaukakarkace ya tsaya. Masha Allah" Cewar Bara'u. Zulƙi ma ya taya shi murna. Nan suka shiga cin masa da miya anaci gaba da hirar duniya da irin yadda zumunci ya taɓarɓare a wannan zamanin da ake ciki. Basu suka fito daga gidan Zulƙi ba sai wajajen goman safiya. Suna tafe sai Gwadabe yace da Bara'u. "Bara'u bayan na gama murnar kyautar da wannan bawan Allah yayi mini. Sai zuchiyata ta shiga canki_cankar shin dawa zamu tafi umararnan Shafa ko Hadiza" Tsayawa Bara'u yayi cak ya zuba ma Gwadabe idanu" Ƙaƙa_sara_ƙaƙa. Ku a tunaninku wacece tafi cancanta a tafi da'ita a babin adalci? A kafta. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 JINJINAR BAN GIRMA A GAREKI MAMAN ANTI , A GASKIYA KIN BAMU NISHAƊI JIYA NAYI DARIYA HARDA FITSARI. DUK WAƊANDA SUKA BADA SHAWARARSU GA MATAN DA SUKE CIKIN MATSALA MUNA GODIYA SOSAI SUMA KUMA SUNCE A GODE MUKU. ZAKU JI YADDA TA KAYA TSAKANIN UWARGIDA MAI AMARYA🤣🤣 NAMA YA DAHU ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU 5 JABBI LAMBA Gari ya waye. Kamar kullum matan gida suna ta hada_hadar data zame musu jiki. Yau Jabu zata fito gobene, jibi ne shirun dai yayi yawa. Yafendo tana zaune tana burga nono tace. "Baɗɗo je ki dubo ƴar uwartaki, yau ko gaisuwar safen data saba zuwa ban ganta ba. Allah dai yasa lafiya" Baɗɗo ta tashi tsulum daga burgar madarar da take yi. Dama itama ƴar uwar tata take ta tunani a zuchiyarta. Tunda ta tashi sai take ta jin faɗuwar gaba. Tana buɗe labulen ɗakin sai taga jabu bata ciki. Ta ƙarema ɗakin kallo komai yananan tsab har gado a lailaye yake, ga ɗankwalin zaninta a saman kujera. Juyowa tayi ta sanar ma Yafendo bata cikin ɗakin ƙila ko ta fita ne. "Kota fita fa kika ce? Tunda Jabu ta shigo gidannan take aure bata taɓa fita daidai da maƙota ba tare da ta sanar dani ba. Kuma kin duba banɗaki ko tana ciki?" "A_a Yafendo bata ciki, sabida su Hassan ma basa cikin ɗakin" Shiru Yafendo tayi. Jikinta dana Baɗɗo duk sai ya mutu. Baddo tana tsaye ta kasa komawa kan aikinta take ita sai taji ma ba zata iya fita tallar nonon ba. Dan tuni jikinta ya bata akwai matsala. Tsulum Yafendo ta miƙe dama da mayafi a jikinta ta dubi Baɗɗo tace. "Taho muje Baɗɗo." A gurguje Baɗɗo ta zare mayafin dake jikin Safiya tabi Yafendo a baya. Sukaita zuba sauri har dai suka isa gidan Dada. Babu fa Jabu babu dalilinta. "Adda Jabu bata zo gidannan ba?" Dada ta miƙe tace. "A_a rabona da'ita tun jiya da daddare dai bayan ta sallami ƴan makaranta. Wani abunne?" Ta ƙarashe maganar a raunace sosai. Yafendo bata tsaya mata bayani ba ta figi Baɗɗo suka soma bi gidajen ƴan uwa ko Allah zaisa a dace. Amman duk inda akaje sai aga batanan. Jikinsu a sanyaye suka dawo gidan Dada. Tana zaune tayi tagumi tunda suka fita gabanta ke dokawa. "Yaya wai lafiya kuyi mun bayani mana wai?" Yafendo ta zauna daɓas ta bata labarin abinda ke wakana. Ƙirjinta ta dafe tace. "Duk yadda akayi dai wata matsalarce. Amman zan shirya in tafi can Kano ko ta tafi can ɗin. Ku kwantar da hankalinku ƙila Kano ta tafi, wala Allah kota gaji da zaman ruga, ko kuma damuwar rashin mijinta." Dada dai batai ƙasa a guiwa ba washe gari ta tafi Kano sassafe. Anan ma dai Yafendo taci gaba da shiga jejuna ko Allah zaisa taga Iyabo. Cikin dare Dada ta isa Kano. Har Iyaa Debisi ta rufe shago sai gata. "Daso kece da daddarennan kuma ke kaɗai babu ɗan rakiya?" Murmushin dole tayi tace. "Toyosi nice kin ganni" "Maraba da zuwa, sannu da hanya" Haka dai suka shiga ciki. Bayan Dada ta rama sallolinta sai suka sake gaggaisawa harma da matan gida. "Toyo Iyabo bata zo gidannan bane?" Iyaa Debisi ta dubeta da kyau ta fahimci akwai fa matsala, sai tace. "Bata zo ba. Amman za'a iya duba gidan Uwani ko tana can. Wani sa'in in ta shigo gari a gidan Uwani take sauka. Ince dai lafiya ko Daso?" "Bafa lafiya ba gaskiya. Yarinyarnan ce dai da sassafe surukarta tazo nemanta wajena. Sannan an karaɗe duk inda ya dace ace an sameta ba'a sameta ba acan. Shine nace bari inzo in duba ko tazo" Ai da jin haka Iyaa Debisi ta shiga ihu tana kwakwazon kiran tashiga uku Daso ta salwantar mata da iyabonta. Kafin kuce kwabo gidan ya cika da matan gidan da samarin gidan. Nan akabar Dada da maimaicin zance. Da Dada, da iyaa Kokodeen, da Iyaa Debisi, da Lekan a daren suka nufi gidan Uwani. Har ta yi bacci taji bugun ƙofa yaƙi ƙarewa ga yarbanci anata yarawa. Jikinta na rawa ta buɗe data fahimci muryar Iyaa Debisi ta jiyo. "Iyaa Debisi kune a darennan, Dada kune?" Jikin Uwani ya mutu murus. Iyaa Debisi tace. "Uwani ko Iyabo tazo gidanki kuwa?" "A_a bata zo ba, ai bata jima da komawa ba" Dada tace. "Kuma ba kuyi waya ta faɗa miki inda zata tafi ba?" Uwani jikinta na rawa sai kawai ta fashe da kuka. Su iyaa Kokodeen suma ai sai suka sau kuka. A darennan hankula sun tashi fiye da tunanin mai karatu. Da Uwani aka kwasa zuwa can gidansu Iyaa Debisi. Kwanan zaune suka yi anata adda'a. Su Debisi dasu Bose, Burodami Kokodeen duk a daren Iyaa Debisi ta tasosu. Washe gari sassafe suka sake rankaya harda uwani akayi Jaɓɓi lamba. Wallahi zancan dai ɗayane babu Jabu babu labarinta. A wannan gaɓar har Dada ta fita hayyacinta ta kwanta jinya. Uwani ce tace zata je Takai in sha Allah ko Iyabo ta tafi can duk da bata tunanin zata je. Iyaa Debisi ce ta hanata tace. "Iyabo ba zata taɓa zuwa Takai ba Uwani ni nasan Iyabo. Abinda za'ayi kawai shine akai report ofishin ƴan sanda, a yi sanarwa a gidan rediyo ko Allah zai sa a dace. Ni damuwata ga goyon yara har biyu. Daso anya kuwa ba kishiyarta bace tayi mata agumu ta cillataba kuwa?" Carab Uwani tace. "Ai babu tantama itace tayi mata wani abun baƙar mitsiyaciya makira. Da wanne irin asirine batai ma Iyabo ba. Balle tana ganin Iyabo ta haifi maza, yaranma ba kifesu akayi a ciki ba" Fashewa da kuka tayi ta kasa ƙarashe zancan nata. Gaga_gaga rikici dai sai ya zama gagarumi su Debisi sune har rugar su Hama. Ai kuwa Hama taci bugu sosai, da ƙyar maƙota suka amsheta. Gaga_gaga akaita tabka shari'a a gaban mai gari. To kunsam sha'ani irin wannan basu da wata hujja na cewar Hama ce taima Iyabo asiri. Kuma ko da kotu zasu je basu da hujjar itace tayi, duk da dai a baya su uwani da Baɗɗo sun kama abubbuwan asiri, shima ba hujja bace da za'a shiga kotu akanshi ba. Maigari ya ba dangin Iyabo haƙuri ya haɗa da rarrashinsu dai haka dole aka fallawama Allah. Kwanansu Iyaa Debisi tara a Jaɓɓi lamba ana abu ɗaya kafin daga bisani suka koma. Dada jikinta yayi mugun tsananin da bata ko iya gane wake kanta. Haka su Uwani suka koma gida basu da yadda suka iya. Sai adda'a kawai suke bin Iyabo dashi. Uwani na shago haka siddan sai ta fashe da kuka. Haka ma iyaa Debisi take yi. Burodami Debisi kuwa kamar zaiyi hauka, shine wancan ofishin ƴan sandan, shine wannan haka yaita sintiri amman jikakeyi shiru malam yaci shirwa. IYABO:. Murmushi nayi ma Batula. Na tsame hannuna a cikin fulawar dana kwaba kusan mutu ashirin ta ɗanwake, hannuna na wanke na nemi gefen tabarmar da take zaune na zauna. To zubo mun tuwon Batula inci maza in koma bakin aikina. Tuwon shinkafa miyar ɗanyar kuɓewa da tsokar kayan ciki da ganda ta zuba mun harda yajin daddawa da man Shanu cokali guda. Ga kuma ruwan kokko kofin roba guda. A cikin gidan akwai masu saida abinci iri daban daban abincinmu na arewa, kuma ko wacce tana da ma,aikata da yawa. Gidan shi yasa kullum a jaƙale kotako ina ruwa, da tulin wanke_wanke. Yawanci wanke_wanken kayan, maza ake ba su wanke tas suma aikinsu kenan biyan wata akeyi musu. To gidan akwai mata sosai dan ko wanne ɗaki cike yake da mata, abun mamaki harda gwauraye masu haya a gidan ɗakin samari cike da gardawa. Ƴan mata da zawarawan gidan masu ido da kwalli ko wacce tana zaune da abinda take ci a matsayin abun karyawanta. Wasu ragowar kaza, balangu, tsiren jiya shi suke ci. Wata kuma taliyar ƴan yara da faidayin wainar ƙoyi. Wata dankalin turawa da tea haɗin murtuk. Wata biredi da bota da wainar ƙoyi. Wata masa da farfesun kan rago. Gasunan dai a jere wacce bata da yadda zata yine take cin duk abinda uwar ɗakinta ta basu amatsayin na karyawa. Batula ma ƙosai da tea da biredi take ci. Ina kan cin tuwona ina danne maiƙon da kokko Zainura ta shigo gidan hannunta riƙe da ledar shopping haka. "Kaga manyan mata sai yanzu kika ga damar shigowa kin dena shakkar Hajja Mama ko?" Cewar Batula. Hauwa dake toya masa sai tace. "Ai da saninta ne shi yasa ta sakankance. Hajja Mama ce ta haɗata da Alhajin. Ni dai a miƙon kasona ina daga nan" Zama Zainura tayi a gefena tace. "Uwar biyu kina fa jina da waɗannan matan." Murmushi kawai nayi mata naci gaba da cin tuwona. Nan Zainura ta raba mana kaza gashasshiya da wani lemun kwali mai shegen daɗin gasken gaske. Ta bamu cake wasu ƙanana, hardama biredi mai kwakwa. Ni dai adana nawa nayi dan na riga dana ƙoshi da tuwonnan na bari da rana maci ni da yara. Fitowa mu ka yi ni da Batula zuwa mami market kasuwar matan sojoji dake gefen barikin dake tsallaken unguwar da muke. "Batula niko mai sunan unguwarnan, naga duk inda muka ratsa hausa nake ji anayi kamar ba kudu ba. Duk da dai akwai ƙabilu amman naga hausawa kamar ma sunfi yawa" Kafin ta bani amsa wani Alhaji ya sha gabanmu da mota. Har Batula ta juya zata sauke mishi tijara sai kuma ta sau dariya. "Yaron waye kyawawa kuka kwaso kuke tafe kuna surutu?" Cewar wannan mutumi yana daga mota ya leƙo da kanshi ta tagarmotar. Batula tace. "Alhaji Ghali kenan. Ga uwar yarannan ka ganta. Ƙawatace sunanta Iyabo bata daɗe da zuwa ba" Sai naga yana bina da idanunshi yana ƙarame zatina kallo. "Wannan irin hannun Dr ce wallahi. Batula abinda za'ayi shine ta bani lambarta zan bama abokina zata ji kira. Kakarta ta yanke saƙa" Batula tayi shewa tace. "Shi Drn yazo da ƙafarshi ya ganta su sasanta. Bawai kai zaka gane mishi itaba" Dariya yayi kawai yace. "Mata iyayen jan aji. To naji in Allah ya shigo dashi zamu tawo ƙafa da ƙafa. Amman alƙawari kar a kuskura ace wani ya rigamu. Dan Dr bazai iya haɗa nema da kowa ba." Kuɗi ya ƙirgo ya miƙo ma Batula tasa hannu ta amshe muka tsallaka. Ni dai bance uffan ba mamaki ya isheni da ganin sarkin fawa sai miya tayi zaƙi? "Dafe kuɗinki Iyabo dan nasan danke ya bayar. In kika bani wani abundai zan karɓa" Ki raba biyu ki bani rabi, tare ya bamu ta dalilinki dan ni ba saninshi nayi ba." Ƙirgawa tayi ta cire nata ta bani nawa. Ta ɗaura da cewa. "Yana da kyau ki sai waya sabida irin wannan rana. Dan nasan baki da wayane na kawar ma da Alhaji Ghali tunani fa. Waya na da amfani. Ko ta dubu ukuce ki samu ki siya ki maƙala sim zawarawanki sa dinga huce miki takaicin ƴan uwansu maza ko me kikace?" Hakane Batula zan siya zuwa ƙarshen wata in Hajja Mama ta bani kuɗin aikina in sha Allah. Haka dai muka shiga wannan kasuwa muka siyo barkono da mai muka dawo gida. Mun dawo mun tadda su Hauwa sun tafi shago. Mu kuma Gaga_gaga muka kama aiki ka'in da na'in. Ina matuƙar jin daɗin zamana a wannan gidan. Musamman in aka zauna ana hirar dare ana shewa wata rana sai a raba dare ba'ai bacci ba ana ɓarin zance. Wata rana darenma ko wacce ta kama gabanta. Haka rayuwata taci gaba da tafiya a wannan gida. Anayin ƙarshen wata Hajja Mama ta bamu kuɗin aikinmu. Dama jira nake yi in karɓi kuɗin in sai sutura ko kala biyu ne. Karfa ku mance kaya kala ɗaya nazo dashi, sai goduwar baƙar rigar kanti da Hauwa ta bani shine kayana suka zama biyu. In ɗaya na jkina ɗaya na shanya. Na gagganɗa da kuɗin dana tawo dashi da yamma Batula ta ɗaukeni muka shiga kasuwar Sms kasuwar suturu kenan. Atampa guda biyu na siya da mayafi. "Iyabo ki sai sim anan in munje gida ina da ƙaramar waya sai in siyar miki dubu ɗaya ma zaki kawo tunda dai kece. Kinga mutane da yawa suna tareni suna buƙatar lambarki, amman sai dai ince musu baki da waya. Shin wai ke ko bakya son yin samari da zawarawane. Ki samu kuɗi ki fantama yadda Allah ya yiki da zatinnan ai wallahi ke kalar matar alhazawace" Dariya nayi mata nace. Ni da nake shayarwa Batula ina ni ina yin wani zawari dan Allah?" Dariya muka yi dukka. Da naci dai Batula tasa na sai sim ɗinnan muna dawowa gida ta bani ƙaramar wayarta aka saka sim na miƙa mata kuɗinta. Washegari ta rakani maƙota na kai ɗinkin kayana. A hanyarmu ta komawane muka ci karo da wannan Alhaji Ghali in baku mance dashi ba, ya sake tsayar damu. Yau ba'a mota yake ba a tsaye suke shida wani dattijo suna magana yaci malum_malum yanata ƙamshi" "Batula ke da matar tamu ce daga ina kuke?" Dariya Batula tayi tace. "Matarku fa? Ku dai tsaya kallon ruwa kwaɗo yayi muku ƙafa. Da kai tunaninka sai taƙi kula zawarawa sabida kace kayi ma abokinka kamu? In ma zai bayyana kanshi ya bayyana kanshi" Shima dariyar yayi yace. "Mufa da gaske muke yi. Yau ɗinnan ma dana je shagon Hajja Mama cin tuwo na mata maganar ai Dr mutuminta ne. Bai shigo bane amman yadai ce babu matsala zuwa ƙarshen wata zai shigo. Matsawar ya shigo zan kawoshi suga junansu. Ko me kikace Iyabo?" Ya jefo mun tambaya. Hakane ai babu komai Allah ya kaimu lokacin da rai da kafiyarmu" "To to ameen nagode. Ga wannan a siyama ƴan biyu alawa" Ya miƙo mun dubu uku nasa hannu na karɓa ina godiya. Mu kai sallama muka shige gida. Gaga_gaga rayuwar taci gaba da gudu dai. Wata ranar lahadi Hajja Mama na gida bata je shago ba sunayin tuhu ranar lahadi sabida jiki da jini. Sai naji ta kirani muna tsakiya da sallamar masu zuwa sayen ɗanwake. "Iyabo kin taɓa magana da Dr ne abokin Alhaji Ghali?" Da sauri na ɗago nace. A_a wallahi ban taɓa magana dashi ba. Ni bamma sanshi ba" Sai tayi dariya da taga na ruɗe tace. "Bawai lefi bane Iyabo ki kwantar da hankalinki. Ai ni ban isa na hanaki kula zawarawa ba. Da dama ni na aurar dasu a gidannan. Da dama yawon bin mazansu suke yi domin samun na rufa ma kai asiri. In kin kula babu ruwana da hana kowa abinda yake so. Ni dai in lokacin aikine ayimun aiki. Sabida haka Dr ya kirani da kanshi yake sanarmun zai shigo yau kuma takanas wajenki zai zo. Zai sauka a zangon baƙi. Dan haka sai ki shirya in ya iso zai kirani sai ki je ki kai mishi abinci ku yi taɗinku acan." Sai naji gabana ya faɗi jikina yayi sanyi ƙalau har ita hajiyan saida ta fahimta" Tofa tashin hankali wanda ba'a sa mishi rana" MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ce. NAMA YA DAHU.... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUDU (6) IYABO:. Hajja Mama ina zan bar yarana to?" "Zaki iya tafiya da kayanki. Zaki iya bama su Hauwa ruƙonsu sai wanda kika zaɓa amman zaki je dole. Hmmm yarinya baki san waye Dr bane, ni wallahi dama naji yace wai takanas wajenki zaizo sai da na girgiza. Zaki iya komawa bakin aikin ki. Kije shagon Bala ki karɓo doguwar riga mai mayafi ƴar kanti da takalmi kice nina aikoki. In kika dawo zaki ƙirga kuɗinshi ki bani. Ki san inda zaki nemi kuɗin da zaki yi mishi girki bette iya bette" Ni dai sukuku na fita na nemi waje sharab na zauna a gefen Hauwa dake ba biyu abinci a baki. "Lafiya Iyabo naga jikinki a mace?" Labari na kwashe na basu ita da Batula yadda mu ka yi da Hajja Mama. Sai naga sunyi dariya harda shewa. Hauwa tace. "To shine duk jikinki ya mace. Ke baki san babban kamu kikayi ba indai Dr na Hajja Mama wanda na sani ne. Harga Allah banyi tunanin a cikin irin wannan layin zai iya ganin mace har yayi tattakin zuwa takanas ba. In dai kuɗin abincine faɗi me kike son girka mishi sai in rakaki mami market mu siyo zan ara miki. Daga nan mu biya wajen Bala mai shago." Hotel fa Hauwa, da yarana kawai sai aga na shige zangon baƙi?" "Ke dallah baƙauya ku wai me kuka ɗauki hotel ne wajen buɗala kaɗai kome? Ke da bakinki kikace zangon baƙi ba zangon buɗala ba. In ba zaki ba sai kije ki sanar mata ai" A_a Hauwa to naji muje mu yi cefanan." Murmushi tayi tace. "Koke fa Iyabo. Da kinata zaune kin ƙi ba kowa dama. Dubi wancan bazawarin na ɗakinsu Habu yadda yake maitar kallonki da son shiga shirginki ke ko ko a jikinki ma. Kasuwa muka shiga muka sai kaza, mai, maggi, shinkafa, sai kayan miya, da kayan lambu. Jallof ɗin shinkafar data wadatu da kayan lambu nayi mishi. Kazar kuma na soyata na sakata a jajjagen attaruhu da albasa. Hauwa ta rakani wajen Bala, ita ta tayani zaɓar rigar ni dai gabana sai faɗuwa yakeyi. Kafin magriba na shirya tsab Hajja Mama ta bani wasu kuloli masu kyau na zuba abincin, na jera duk abinda ake buƙata a 🧺 basket. Ina yin sallar magriba naji Hajja Mama na waya dashi akan ya iso yana hotel ɗin daya sauka. Ga Alhaji Ghali yana ƙofar gida zai kawo ni. Wallahi da ƙyar na idar da sallar, ina idarwa na shige banɗaki a guje sai gudawa. Ina jiyo Hajja Mama na zage_zagenta ni dai jikina na rawa na fito. Ina ji ina gani na fita na bar yarana. Hauwa ce ta biyoni da gudu. "Iyabo kifa saki jikinki meye haka tun a gida kinga yadda jikinki ya mutu kuwa?" Ni dai bance da'ita komai ba nayi ficewata a bakin motar Alhaji Ghali na tadda Batula sunata hira da dariya. "Yauwa matarmu masha Allah. Muje ko? Batula mu sai mun dawo" "Iyabo sai kun dawo, kya gaishe da Dr ɗin" Kai na ɗaga mata kawai, na shiga bayan mota tare da basket ɗin. Muna tafe gabana na tsananta bugu har Allah yasa muka isa HOTEL ɗin. Get ɗinshi a wangale dama yake. Ni dai ina biye da Alhaji Ghali a baya. Basket ɗin abincin na hannunshi har muka tsaya a daidai room 11. Ƙofar ya ƙwanƙwasa daga ciki muka jiyo ance. "Ghali shigo mana, ai tun isowarku na hangoku ta taga" Ghali na gaba ina biye dashi kaina a sauke" "Madam ga bakin gado yi zamanki bari in watso ruwa in fito. Alhaji Ghali zaka jirani ne?" "A_a na cika aikina sai mun haɗu gobe kawai" "To ni gobe jirgina 7 na safe zai tashi kasan sabida inga gimbiyane nazo ai.' Ni dai ina ɗofane a bakin gadonnan kaina a ƙasa ina jinsu, amman wallahi har lokacin bansan kalarshi ba dan ban yarda na kalleshi ba. "Gimbiya bari in sallami Ghali in ba haka ba bazai barni ba kinji?" Yayi magana cikin taushi. To babu damuwa " Kaɗai na iya cewa suka sa kai suka fice. Sai lokacin na sauke ajjiyar zuchiya na ƙarema haɗaɗɗen ɗakin kallo. Wayarshi aketa kira tunda suka fita wayar na gefena naga an rubuta lovi_lovi matarshi ce kenan take kira. Da sallama ya shigo ɗakin ya zauna akan ƙaramar kujera. "Gimbiya bani wayarnan yara sai damuna da kira suke yi" Wayar na ɗakko na miƙo mishi sai naga hannunshi fari sol sosai. Ni dai inaji yana waya da matarshi sai lokacin na samu zarafin satar kallonshi. Dattijone ba sosai ba, gashin ƙasumbarshi, da gemunshi rabi fari rabi baƙi, haka ma sumar kanshi. Saye yake da shadda waganbari mai ruwan makuba ta amsheshi sosai. Yana gama wayar yace. "Kin ƙi ɗagowa ki kalleni ma. Wai a haka zamu yi zancan kenan uhm Iyabo" Ni dai nayi murmushi sai na ɗago muka haɗa idanu, nayi saurin kawar da kaina. "Masha Allah. Ina godiya da Allah yasa banyi fatali da zaɓin Ghali ba. Da farko sunana Dr Usman bin Usman. Shekaruna Hamsin da shida. Matana biyu yarana huɗu biyu maza biyu mata. Ni likitane ɓangaren masu matsalar ƙwaƙwalwa. Ni ɗan garin Gombe ne bafulatanin usil. Zan so ji daga gareki. Meya fito dake a gidan mijinki ke? Kaina na sauke ƙasa kawai. Sai ya jawo baske ya zuba abinci, ya yi loma ɗaya kafin yace. "Ke nake saurare" Komai a nutse yake yi sosai. Yana magana yana lumshe idanunshi. "Sunana Iyabo kamar yadda yazo maka. Ina da yara biyu Hassan da Usaini shayar dasu nake yi. Abinda ya shafi rayuwa ta baya kuma babu abinda zan iya sanar maka kayi haƙuri dan Allah" "No kar ki bani haƙuri babu komai ai. Koma dai menene ina sonki a hakan. Ni kuma aurenki zanyi mu ba yara bane balle mu tsaya wani zance ko waye_waye. Bama ni da lokacin hakan sam. Ɗan Lokacin nawa iyalina nake bama suma su ji daɗinsu. Da fatan nayi miki an amshi tayina, in kuma kina da wanda kike so kar ki ɓoye mun komai Iyabo danni ban iya son abuba in ina so" A_a banda kowa. Kuma na amshi tayinka Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi. Sai dai yarana ƙanane sosai Mama suke sha" Dubana yayi yana murmushi yace. "Hakan matsalane a wajenki? Ni a wajena babu wata matsala. Amman bansan mai kike tunani ba uhm?" Numfashi naja nace. Dama naso in yayesu ne tukunna dai. Sannan ina da tambaya" Dariya yayi, sai da ya cinye abincin bakinshi kana yace. "Yi tambayar tukunna' Me yasa kake sona, sannan mai yasa har abokinka yasan irin macen da kake so?" Dariya yayi sosai. Ni kuma saina shagala da kallonshi. Dattijantaka tayi mai kyau, nutsuwa ya ƙara haskashi. "Iyabo kenan. Ghali abokinane sosai. Yanayin aikine yasa bamu fiye haɗuwa ba. Ɗakinmu ɗaya a makarantar bording da muka yi. Tun muna wannan matakin yasan inason mace mai jiki, kuma ƙabila. Matana kab babu bahaushiya. Sai dai basu da ƙiba su gaskiya, yanzu ne dai na samu cikar burina Kar kiyi tunanin ko sha'awar jikin nake yi. A_a Allah ne shaidata halittatace mai son mace mai ƙiba. Zancan son mace ƙabila ya ɗakko asaline babba wanda na miki alƙawarin haɗuwa ta gaba zan faɗa miki. Nagode da abinci. Muje in kai ki gida gobe zan koma Gombe. Miƙewa nayi da sauri damar kamar a ƙaya nake. Muna fita na sauke wawuyar ajjiyar zuchiya. Muna tafe a jere ga basket ɗin abinci a hannunshi har gaban wata baƙar mota. Da kanshi ya buɗe mun murfin ƙofar har saida na shiga ya kulle kana ya zagayo ɓangaren matuƙi ya shiga ya ja motar. "Ina wayarki in saka miki lambata?" Ƴar ƙaramar posar dake hannuna na zaro wayar na miƙo mishi. Wayar yaita jujjuyawa dai, bai bani ba bai saka number ba har muka iso wani shopping moll babba. "Ki jirani ina zuwa, ko kina so ki bini?" A_a zan jiraka" murmushi yayi mun kawai ya tafi ya barni. Idanuna na lumshe. Indai miji nake nema to Usman bin Usman yayi. Allah yasa ba yaudarata zaiyi ba. Duk da dai bai taɓa jikina ba sam. Ina wannan taɗin zuchin na hangoshi da ledoji riƙi_riƙi ya jibgesu a bayan mota ya shigo. "Aimun afuwa inna daɗe" Dariya kawai nayi ni dai muka kama hanyar gida motarshi har ƙofar gidan. "Bana so mu rabu, inaga zan ɗaga tafiyar sai jibi, gobe zan zo in ɗaukeki da yaran muje yawo ko?" Idanuna na lumshe. A zahiri Usman yana da baiwar nutsuwa, sannan ni dai lokaci ɗaya na kamu da sonshi, kundai san halin zuchiyata itance ba'a canjata ba. To Allah ya nuna mana goben. "Goben zan sake sanar dake abubbuwan daya dace ki sani a kaina ko?" Kasa magana nayi dan sai kallona yake yi. Wayarshi ya ciro ya cire sim ɗin ya mayar da sim ɗina ciki. Da wayar tashi da tawa wayar, da katinshi duk ya miƙo mun. "Ga katina akwai lambata a jiki. Ga wayata kiyi amfani da'ita, ni nayi amfani da ɗayar." Hannu yasa a aljihu ya ciro rafar ƴan ɗari bibbiyu sababbi ya miƙo mun rafa ɗaya. "Wannan kuma sai ki loda kati. Ga tsarabar ƴan biyu a bayan mota bari in tayaki fitowa dashi. Amsar kuɗin nayi nayi godiya sosai. Har ƙofar gidan ya rakoni da ledojinnan. Hannu nasa na amsa nace. Allah ya tsare hanya, saida safe nagode " Ban jira amsarshi ba na wuce harna kusan ƙulewa saina juyo. Usman na tsaye ya nannaɗe hannayenshi a kirjinshi yana ta aikin kallona. Baka tafi ba?" "Sonki ya hanani tafiya. Bazan ɓoye miki ba kin samu gurbi mai kyau a zuchiyata. Ina fatan za'a tausaya mun" Murmushi nayi mishi nace. Baka da matsala zuchiyarka tazo hannun da akasan mutuncin so. Ka daure ka tafi dare nayi saida safe." Na jiya na shiga cikin gida da sallama. Duk suna baje a tsakar gida na shigo kiki_kici da ledoji. Batula da Hauwa suka yo kaina da oyoyo harda tafi. Duk suka amshe ledojin suka nufi ɗaki. Da sallama na shiga ɗakin nima Hajja Mama na waya na zauna a gabanta. "Kar ka damu Dr yadda kake so ai haka za'ayi likita bokan turai. Gata ma yanzu ta shigo bari in turota" Ƙit ta kashe wayarta.. "Tashi maza Dr na waje wai kinyi mantuwa. Ke yarinya ke kika iya shigowa Lagos. Ke daga gani ƴar albarka ce kin rabu da iyayenki lafiya." Ni dai tashi nayi na koma, yana tsaye inda na barshi. Assalamu alaikum" Nayi mishi sallama ya amsa a hankali. "Kiyi haƙuri zaki ce na fiye naci ko? Wallahi baki mance komai ba so nake in sake dai ganinkine" Murmushi nayi, shima murmushin yake yi mun. Mun sake jimawa muna hira kafin dai na samu da ƙyar ya tafi nima na shige gida. Kuɗin daya bani na miƙa ma Hajja Mama. "Kuɗin Bala kawai zaki cire ki bani. Ki adana kuɗinki, a cikin ledojinnan dai a zazzage in zaɓa" Na ƙirgo kuɗin Bala na bata. Hauwa ma na bata kuɗin data aramun kana na zazzage ledojinnan. Ledar farko kayan kwalliyane da turaruka. Leda ta biyu kazace gashasshiya, sai cake da lemukan kwali. Ɗayar ledar kuma biskit ne manyan da alawa kala_kala. Kayan kwalliyar Hajja Mama ta ɗiba kawai, kazar ma tace ba zata ci ba. "Yaya kuka yi dashi to?" Cewa yayi shi aurena zaiyi. Amman na faɗa mishi da so samune inaso in yaye yarannan tukunna. Sai yace shi ta ɓangarenshi ai babu wata matsala" "Da kinsan waye shi ƙila da in yau tace a ɗaura auren zaki yadda. Wallahi ni da farko nayi tunanin ko sha'awarki ce kawai yake yi, duk da nasan ba mutumin banza bane gashi da kulawa da iyali. Ai kinanan na haɗa ma matarshi akwatunan suna kuɗi ya kashe mata sosai da sosai. Ki nutsu ki kamashi, ɗan kiran waya, ɗan tura saƙon Barka da da safiyannan, dan kirsa da kisisinannan duk kar kiyi wasa kinji ko" To Hajja Mama in sha Allah. Na kuma gode sosai." Na kwashe kayana ɗan ƙwalam da maƙulashenmu muka ci ni da su Hauwa, ƴan biyu kuwa sunyi baccinsu. Kunga wayar ɗaya bani, tashi ce ma ya zare sim ɗin ya mayar da nawa." Batula ta fisge wayar tace. "Black berry razor? Tabb wannan wayar ta manyace sosai. Gaskiya Ghali yayi miki babban kamu" "Ku mu kwanta kar gobe mu kasa tashi" Ni dai har su kai barci idanuna biyu ras sai juyi nake yi ina tuno Usman ina murmushi. Bansan sanda bacci ya kwasheni ba sai ji kiran sallah kawai nayi. Ina miƙewa sai ga kira ya shigo wayar. Lambar naketa kallo kafin na ɗauka na kara a kunnena" "Amincin Allah ya tabbata a gareki gimbiya. Da fatan kin tashi lafiya ko?" Idanu na lumshe kana nace. Ameen tare da kai. Da fatan kaima ka wayi gari cikin ƙoshin lafiya?" "Uhm lafiya ba lafiya ba dai" Dariya mu ka yi duka kafin ya ɗaura da cewa. "To cikin tunaninki na kwana. Yadda kikasan lokacin aurena na fari. Juyi fa na dingayi ina tunaninki da furfurata. Gashi bazan samu damar tsayawa kamar yadda na alƙauranta miki ba. Da asufa suka suka ni daga can Gombe yarona ba lafiya sun kwana yana suma. To shine nake son inje inga halin da yake ciki. Duk mun shiga tashin hankali." Assha Ubangiji Allah ya bashi lafiya. Yarone ƙarami?" "Uhm jinjirine ma, uwar ta kirani sai kuka take yi. To zan dai wuce zuwa anjima inna sauka zamu yi waya. Ki shafa mun kan yarana sai anjima" Sallama mu ka yi na sauke wayar a kunnena nayi saurin tashi na ɗauro alwala na yi sallah. Biyu suka far mun da tsotso da ƙyar na yakicesu na nufi bakin aikina. Yau dai cikin farin ciki sosai na wuni zuchiyata fes. Minti_minti sai Usman da murmushinshi ya faɗo mun. Gashi har magriba tayi bai kirani ba balle inji yaya ya samu masu jiki. Ina zaune ina cin shinkafa da miya da latas Batula ta dawo daga unguwa hannunta riƙe da leda ta nemi waje ta zauna. "Kin ko kira Dr a waya kinji ya mai jikin?" Ajjiyar zuchiya na sauke kana nace. A_a tsoron kira nake yi ko yana tare da matarshi kinga ai ba zata ji daɗi ba ko? Amman tun ɗazu nake jiran wayar tashi" "A_a ba haka za'ayi ba to. Ki rubuta mishi saƙo ki tura mishi zaifi sauƙi" Ai kamar gara kiran wayar ma ko. Kinga bana son haddasa wata fitinar bari dai in kira" Na danna lambarshi na kirashi. Ai kuwa ringing biyu sai ya ɗaga. Wata ajjiyar zuchiya ya sauke mun kafin yace. "Ai da harna soma fargabar ko dai ni kaɗai nake kiɗana da rawanane ashe ba haka bane" Murmushi nayi mishi nace. Ba haka bane, ya mai jikin ka sameshi, da fatan ka sauka lafiya?" "Jikin da sauƙi yanzu na baro asibiti. Dama na barine inna gama magana da Alhajinmu inna fito in kiraki kafin in wuce gida, sai kika rigani" Daga haka muka ɓalle da hira dai, kafin daga bisani mu kai sallama. Sai yanzu hankalina ya kwanta. Batula na kamu da yawa wallahi" Dariya tayi mun. "Ai dole ki kamu Hajiya. Kinga muci kaza ki ajjiye wannan jiƙaƙƙiyar shinkafar. Ko ba shinkafar Anty bace? Ai bata iya girki ba ku da kuke siya kuna ƙoƙari. Ni dai ta baje mana kwaɗayi mu kai tayi. Gaga_gaga al'amura suka ci gaba da kankama a cikin kwana goma ni da Usman mu ka yi wani irin shaƙuwa na mamaki. Na fahimci yana mugun son soyayya ashe gaskiya ne da akace dattijai mayun soyayya ne. Yau mun wayi gari ina da babban baƙo a hanya. Tun safe ni da Batula muke ta girki dan ya sanar mun ƙarfe taran safe jirginsu zai sauka kuma abincina yake son ci. Wannan karon jallof ɗin couscous nayi mishi mai wadatar kayan lambu da anta. Sai soɓo mai abarba da kankana. Taran nayi ya kirani yace jirginsu ya sauka. To Shikenan ganinan zuwa ni da ƙawata Batula zata yi mun rakiya, zata taya ni dakko maka yaranka" "To tunda hakan kika tsara amman da ai gidan zan shigo kawai ma ba sai anga matata na sunturi a hotel ba ko?" Sai kunya ta kamani nace mai. To Shikenan bari in sanarma Hajja Mama, sai ka iso" Ina ajjiye wayar na shiga uwar ɗakin Hajja Mama na sanar mata yadda mu ka yi da Dr" "Wannan gidan namu zai shigo? Lallai Dr ke kam yana ji dake. Shi da ko unguwarnan tamu baya iya shigowa sai gashi Dr yau shine zai zauna a ɗakina? To mu yanzu zamu tafi shago in ya iso ki shigo dashi cikin uwarɗakina. Amman yana tafiya ki kullemun kar aimun sace_sacen da aka saba" Kwaɗo da mabuɗin ta bani suka fice a gidan. Sake gyara uwarɗakin nayi duk da dai fes yake nice harda kunna turaren tsinke. Awa biyu sai ga waya yana ƙofar gida in fito in mishi iso. Tashin hankali wanda ba'a sa mishi rana. Iyabo tayi bazawari ɗan soyayya, itama ta kamu da son shi. Gata da aurenta wannan masifa da mi tayi kama. Mata masu bin bokaye wallahi muji tsoron Allah. Ina Hama zata kai girman wannan zunibin nata duk akan rijalu? Ya Allah kasa mufi ƙarfin xuchiyoyinmu Ameen. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU (7) GWADABE:. "Kai a naka dawa kaga yafi dacewa kaje a babin adalci a cikinsu wacece tafi kyautata maka tafi son abinda kake so?" "Kai tsaye Shafa ce. Hadiza fa dan dole nake zaune da'ita. Jibi jiya ana hira ana dariya sai taɓe bakinta yarinyarnan take yi. Ta ɗauki kishin duniya ta ɗaura akan Iyabo. Ita tana gidan ɗan fulaninta abunta." Bara'u yace. "To a gaskiya ka tafi da Shafa kawai, ni fa amman shawarace. In kuma kana gudun matsala yi ƙuri'a duk abinda suka ɗauka sai ka ɗauki dangane. A babin maslaha kenan wannan. Amman zanso ace Shafa ta ɗauka ko dan albarkacin kawaici da Iyabo da take goyama a bayanta" "Wallahi nima haka. Bara'u ina ma Shafa so mai kyau mai haɗe da mutuntawa da darajawa, ita gani take nafi son Hadiza, a zuchiyata kuma ba haka bane. Wallahi in ranta ya ɓaci sai inji har shakkarta nake ji, kuma fa bawai zata yi mun magana bane. Itace makwafin Iyabo wajen haƙuri. Yarinyarnan Iyabo da take goyo ina jin sonta sosai dannewa kawai nake yi." Bara'u ya kwashe da dariya suka tafa. "Wallahi Gwadabe kai mugun ɗan iska ne. Mata na gidan aurenta ka kasa haƙura da'ita gaka da mata ɗanɗasa_ɗanɗasa itama Shafa naga sai fashewa take yi dan na fahimci kanason ƙatuwar mace mai jiki zaz tsoka. Dariya suka saka harda tafawa. A gidan iyayen Bara'u suka samu suka shiga suka yo wanka sannan suka shiga ɗakin zaure suka sake kaya gidan suna cike da mutane maƙil. Bara'u ne ya kirawo Sakina mai jego tasha kyau. "Ki karama Gwadabe matanshi su sameshi a ɗakin zaure. In abinci yayi a tawo mana dashi." "To amman Bara'u kayan cikin tunkiyarnan yayi kaɗan an soyashi baka ganshi ba, nace ko za'a ƙaro mana naman kasuwane?" "Ni ina naga wani kuɗin Sakina. Kajinnan guda huɗu dake cikin keji kisa a yanka sai ku haɗa ai dai shikenan ko?" "I shikenan zansa Alawiyya ta ƙaro mun biyu ana Ummanmu su zama shida sai a haɗa. Bari in turo maka su. Dama Hadiza taƙi sakewa sai takure kanta takeyi. Ni naga duk ta lalace ta dena gayen ma ta ɗaurama kanta kishi mai tsanani." Harararta Bara'u yayi yace. "Nima ai auren zan sake in sha Allah. Tunda Gwadabe yayi biyu nima kinsan sai nayi" Dariya tayi harda guɗa. "Allah dai ya kawota lafiya. Kaine dai sai mu rabaka biyu ko wacce taja nata. Ni wallahi sai in barma amarya kai kacokan in rungume ƴaƴana." Nan ta wuce Bara'u tayi cikin taron mata. Bara'u na ba Gwadabe labarin diramar da suka yi da Sakina sai dariya suke ƙyaƙyatawa sai ga Shafa ta shigo da tran abinci niƙi_niƙi ta dure, ta sake fita sai gata da ruwa. Iyabo ta miƙa ma Gwadabe yayi maza ya amshe abunshi ya rungumeta. Bara'u daya ɗebi abincinshi sai ya bashi waje. Shafa ta zuba ma Gwadabe abinci ta saka cokali ta ɗebo ta kai bakinshi kenan Hadiza ta shigo riƙe da ɗiyarta. Tana ganin haka ta sake murtuke fuska. Shafa ta sake ciko cokali ta ba Gwadabe. Hadiza ta kai iya wuya dan ko nunawa ba sui sun gane tana ɗakin ba sai wani taɓa shi Shafa take yi, itace harda goge mishi baki. "Ko dai inje ne in kuka gama taɓarar ni sai in dawo." Gwadabe cikin cusa haushi ya kalleta yana zare idanu yace. "Ya ilahi baki ga abinci nake ci ba, ko so kike saina ƙware? Sannan da kika shigo wa kika kula ma? Hadiza ta dubeshi tana mamakin akan Shafa ne yake yi mata haka. Kai kawai ta girgiza ita kuwa Shafa sai ciko cokali take tana bashi ga wata dariyar iskanci da suke ta yi. A fusace ta miƙe har ta sa ƙafarta ɗaya a waje Gwadabe yace. "Kul kika sake kika fita na faɗa miki kenan. Shin ke a komai sai kin nuna rashin haƙurinki ne mtws?" Kamar dai ba zata dawo ba sai dai ta dawo ta zauna. Hannunshi ya dunƙule ya miƙama Hadiza yace. "Zaɓi ɗaya hagu ko dama?" Hannun ta ƙarema kallo ta rasa wanda zata ɗauka. Sai kawai tace. "Shafa ta soma ɗauka" Gwadabe ya miƙa ma Shafa hannun sai tace ta zaɓi dama. Hadiza tace "Na ɗauki hagun" Ware hannayen yayi ya nuna ma ko wacce abinda ta ɗauka. "Ke me kika ciyo Shafa?" Tana dariya tace. "Tafiya naci, wayyo Allah daɗi mijina" Murmushi yayi yaji daɗi sosai da abinda Shafa taci har ga Allah da ita yake son tafiya. Hadiza kuma ƙwafa tayi tana hawaye tace. "Wallahi, wallahi bazan yadda ba. In Qur'ani zaku haɗiye kuna aman ayoyi bazan yadda ba bakinku ɗaya ba. In dai adalcine dani ya dace ace an tafi babu wani ƙuri'a." Murmusawa Gwadabe yayi yana kallonta da mamaki yace. "Hadiza kenan. Ai ko a gidanku malam da ƙuri'a aka san shi. Kuma bai taɓa sauya wadda taci ba. Na lura ke dai bakya son ganin ana zaune lafiya. Ba dan ina jin tsoronki ba zan yi ƙuri'a a takadda ku sake zaɓa duk wacce taci itace kawai." "E na yadda da hakan. Amman wannan kam ban yadda dashi ba ina." Gwadabe ya girgiza kanshi kawai ya nufi wajen akwatin ƙarfen dake ɗakin ya yagi takaddu ya yi rubutu ya dunƙule ya kawo musu. Hadiza sai girgiza take yi tana ciccika tana babbatsewa. "Ke ki soma ɗauka" Cikin fishi ta warci ta gaban Shafa." "Allah ya kyauta" Cewar Shafa. Ai sai Hadiza ta daki ƙirjinta tab tace. "Ya kyauta abunda yafi haka ƴar abu ta kazan...." Gwadabe yasa hannu ya tsinka ma Hadiza mari lafiyayye. Ya dubi Shafa yace. "Yi haƙuri My love, baki ji dai ciwo ba ko?" Murmusawa Shafa kawai tayi. Hadiza kuwa tuni ta shiga taitayinta tana dafe da kuncinta tana ma Gwadabe kallon mamaki. Shi ko sai hura hanci yake yi. "Shafa ɗauki naki. Ko wacce ta faɗi abunda taci" Shafa tasa hannu zata ɗauka kenan Hadiza ta ajjiye wanda ta ɗauka ta warce wanda Shafan zata ɗauka. Gwadabe ya taɓe bakinshi kawai. Shafa tace. "Tafiya na ɗauka" Ai sai Hadiza ta fashe da kuka ta miƙe da ƴarta a hannunta. "Shikenan ka nuna mun matsayina a wajenka. Ka fifita Shafa a kaina. Da ita kake so lallai kayi tafiya. To ni dai sai dai ka sauwaƙe mun wallahi Allah na gama aurenka tunda har ka iya dukana a gaban wannan yarinyar. Ga atampar da mitsiyaciyar matarka ta bamu banso" Ta kwaɗo mai atampar a fuskarshi tab. Idanu ya lumshe yana ambaton Allah dan wallahi ji yake yi kamar yaita dukan Hadiza a ɗakinnan haka yake ji. Shafa ce tayi saurin riƙe hannunta hankalinta a tashe. "Sakemun hannuna dan kutumar.... Ta mulmulo zagi ƙato ta cunkusama Shafa. Cikin wata iriyar tsawa Gwadabe yace. "Ki sake ta ta tafi nace miki kafin in illatata a ɗakinnan dan wallahi zan iya nakasata" Tsawar ta gigitasu dukkansu da sauri Bara'u ya shigo ya tadda su a birkice. Bangazarshi Hadiza tayi ta fice. Sai gata da akwati tazo wucewa Sakina sai magana take yi mata taƙi saurarenta. Haka Bara'u ya bi Hadiza waje shima da sauri. "Ungo yarinyarnan ki shiga gida. Sannan ki soma shirye_shirye umara zamu tafi" Shafa ta buɗe baki zata yi magana Gwadabe ya mata wani kallo. Muƙut ta haɗiye maganarta ta karɓi yarinyarta ta koma ciki. Sakina tace. "Gwadabe a riƙa haƙuri kasan sha'anin mata sai haƙuri. Duk da dai Hadiza kam tana da matsala. Tun dai da aka ambaci Iyabo, tare da gabatar da tsaraba shikenan na kasa gane mata. Ko aikin girki taƙi yi, sai tunane_tunane take yi. Ayi haƙuri amman ko dan gudun lalacewar zumunci. "Babu komai Sakina nagode. Kuci gaba da taronku bari in je in samu Bara'u ' Yasa kai ya fice kiciɓus sukai da Bara'u a ƙofar fita. Hannunshi ya jawo suka nemi ƙarƙashin bishiya suka zauna a kututture. "Tabb yau ni naga kishin mata. Yarinyarnan yi tayi kamar fa zata zageni. Dan idanunta gaskiya sun gama rufewa. Tayi tafiyarta abunta taƙi fur ni kuma ba matata ko ƙanwata ba balle in jawosu da ƙarfin tuwo ba. "Rabu da'ita Bara'u. Gara data tafi dan in ina ganinta zan iya aikata abinda zaku yi mamaki. Kasan menene tun kafin Hadiza ta sani cikin uku zan yima tubkar hanci ai banji a jikina zan iya ci gaba da rayuwa da'ita ba. Gobe sassafe zamu juya muma. "Kai abun ya matuƙar bani mamaki yanzu abinda zamu yi muje masallaci muyi sallah sai mu ci gaba da tattaunawa " A masallacin jikin gidan Zulƙi sukai Sallah Zulƙin ma ya fito tare dashi akayi sallar. A cikin masallacin harda Da'u sai kallon Gwadabe yake yi. Gwadabe ma yana ta kallonshi yadda kuka san bai gane Da'u ba. Sai dai a ƙasan ranshi tausayin Da'u ne danƙare a ranshi ganin yadda ya rame ya fita hayyacinshi. Shi ko Gwadabe yana cikin shiga ta alfarma kallo daya zaka yi mishi ka gane yana cikin kwanciyar hankali. Jikin Da'u a mace ya fita daga Masallacin ya juma a jingine a ƙarƙashin bishiya yanata tunanik ko ya koma su gaisa da Gwadabe ne ya faɗa mishi Babala bata da lafiya? Wata zuchiyarce ta gargaɗeshi da yin hakan yana gudun kar Babala tayi fishi dashi, dama yanzu hakan ma a cikin fishi dasu take tana faɗa musu sun gaza a kan lafiyarta. Tunda dai Yaya Hambali ya ƙwace dukiyarshi daga garesu Babala ta juya musu baya suma matansu da yaransu suka kasance abun kyara kamar Iyabo a da. Gwadabe dai suna zaune har Zulƙi ya salllami jama'a ya dawo wajensu Gwadabe. "Yaya ake ciki ne, wanne hukunci ka yanke Gwadabe munyi waya da maigidana yace in kawo ka" Idanu Gwadabe ya lumshe yace. "Na amince Zulƙi. Amman sai dai haɗuwar ta zama yau in Yana da lokaci matsalace na iyali ya taso gobe nake son in juya" Zulƙi yace wannan babu wani matsala. Bari zuwa bayan magriba ai sai muje mu ganshi ko Bara'u. A tsaida magana ka cike form na jam'iyya shikenan ka zama member. Sai dai fa kaga lokacin ya kusan gabatowa an riga an kaɗa gangar siyasa ba zaka samu lokacin kan ka ba, kaine meeting a Abuja, kaine meeting a cikin Kano haka za'aitayi. Sannan zamu samu malamai da zasu dinga mana adda'a akan lamarin". "Duk babu wata damuwa. Allah dai ya nuna mana lokacin. A daren su Gwadabe suka shirya zuwa gidan Chairman na nan Takai sun shafe tsawon awa uku cib suna meeting. Daga ƙarshe komai ya daidaita ya ɗebo kuɗi ya ba Gwadabe yace ya soma riƙewa a hannunshi na ɗinke_ɗinken suturu. Godiya sukai mishi suka yi mishi sallama. Kai tsaye Zulƙi ya kai Gwadabe gidan shugaban party na nan takai akai mishi rijistar ya zama member. Washegari Gwadabe ya je gidansu Shafa ya ɗauketa suka kama hanya dan jiya a gida ta kwana. Cikin dare sosai suka isa, dalilin da yasa Gwadabe bai je wajen malam ba kenan. Sai da safe bayan ya gama kintsawa harda jakar magungunanshi ya rataya sai ya shiga gidan har turakar Malam. Hadizan tana ciki Malam da su Baba Suwaiba sun tusata gaba anata mata faɗa harda Yaya Tasi'u da Yaya jamilu. "Yauwa Gwadabe shigo ashe ka dawo?" Cewar Malam kenan. A hankali Gwadabe ya shiga ya durƙusa ya gaishesu ɗaya bayan ɗaya kana ya nemi waje ya zauna. "Gata tunda ta dawo ake tuhumarta dalilin dawowarta dan tayi fur taƙi komawa ɗakinta. A ɗakin Asshi ta tare. Yau da safennan Sabitu ya mammaketa da ƙyar iyayensu mata suka karɓeta. Tunda dai gaka ko zaka iya faɗa mana menene ya faru?" Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke yace. "Wallahi Malam tunda dai na auri Hadiza bata barni na shaƙi iska ba. Ƙorafin yau daban na gobe daban. Lallaɓata dai kawai nake yi shi yasa ba'a jin kanmu. Wasu daga cikin manyan abubuwan da tayi kun sansu. Da yawan wanda take yi ko abokiyar zamanta bata sani ba. Nan Gwadabe ya kwashe kab irin rayuwar da suke yi ya faɗa ma Malam da musabbabin abinda ya kawo wannan matsalar da har tayi zuchiya ta kamo hanya. Salati duk mazauna dakin suka kama banda Gwadabe da Hadiza da suke kallon kallo. Sabitu ya fashe mata bakinta har ya ɗan kumbura. Kai malam ya girgiza yace. "Kayi ƙoƙari kayi zumunci, kayi kuma kawaici. Ke kuma Hadiza kin kyauta sosai da abinda kika aikata. Nayi imani da mahaifiyarki tananan da kin gama bata kunya. Gwadabe tun farko abinda na jiye maka kenan game da Hadiza bayan kayi mun bayanin Shafa. Ni ubanka ne bazan so yadda gidana yake a da inso naka gidan ya zama irin nawa ba. Sabida haka ka saki Hadiza ka huta ta huta umarni na baka. Itama sakin take so dan tayi ma Asshi rantsuwar matsawar da Shafa zaka yi tafiyarnan to sai dai ka rabu da'ita. Kuma tunda Shafa ta ciyo tafiya dole ku tafi. Ina taya ka murnar samun damar ziyartar masallacin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama da zaku yi. Bata takaddarta" Ai sai kuka. Ɗakin yayi tsit baka jin sautin komai sai sautin kukan Hadiza daya cika wajen. Shin kukan baƙin cikin umarar da za'a tafi da Shafa take yi, ko kukan baƙin cikin rabuwa da Gwadabe ne, koko kukan farin cikin rabuwarne ita ta barma kanta Sani Baba Asshi tace. "Ayi haka Malam ayi tunani kar hakan ya taɓa zumunci gaba" "Babu wani zumunci da zai taɓa Gwadabe dai ɗanane, itama Hadiza ƴatace to wa zan yar cikinsu? Ai ci gaban zamansu ne zai iya raba zumuncin. Dan haka ya saketa ta tattaro mishi ƴaƴanshi ta bashi dan gidan zata bari ma" Da sauri ta ƙarasa gaban malam ta rirriƙe ƙafafunshi tana. "Kaimun rai Malam wallahi inason mijina" "Ko ki cika mun ƙafa ko in kira Sabitu dodon naki ya daka mun ke. Ai wallahi kinji na rantse aurenki da Gwadabe yazo ƙarshe. Kuma in da wannan halin zaki sake shiga gidan aure shima koroki zayyi kinga shikenan kin zama abinda kika zama." Da sauri ta saki ƙafar malam da taji ya soma kiran Sabitu. Matan Malam dai basui yunƙurin sake tausar malam ba dan sunji ya rantse sun san bazai yi kaffaraba. "Na sake ta saki ɗaya" Gwadabe ya furta a sanyaye. Malam yace. "Allah yayi maka albarka maza tafi nema abunka" Tashi yayi ya fita, da gudu Hadiza tazo ta wuceshi Ashe Yaya Tasi'u ne ya biyota da gudu suka burma ɗakin Baba Asshi. Gwadabe ne ya bisu da gudu shima. Da ƙyar Gwadabe ya kwaci Hadiza a hannun Yaya Tasi'u. Ranar dai har Gwadabe ya dawo aiki yanata aikin tunani gami da jin kunyar Malam da su Auwala. Dan yana dawowa Shafa ke sanar mishi Hadiza babu lafiya. Tare suka shirya suka je dubota daga nan suka wuce su ka yi paspo na tafiya. Kwanan Hadiza bakwai aka sallamota a asibiti. Sai lokacin Gwadabe ya durƙusa a gaban Malam yake shaida mai labarin siyasa da takarar da akeson ya fito. Da ciwon da Babala tayi. A lokacin Babala ta warke har an sallameta ma kuma Gwadabenne ya ɗauki nauyin komai da komai nata. Malam yayi murna sosai ya saka albarka a cikin lamarin ya sake da jinjina ma Gwadabe akan abinda yayi ma Babala. "Malam sai maganar Hadiza dai" "Kai ya isheka nace maka. Hadiza ko zaka dawo da'ita ka barta a yanzu ta horu tukunna. Inayin hakanne ɗomin in kawo maka ƙarshen matsalar gidanka. Hadiza in ba da gaske akayi mata ba ba zata barka ka sha ruwa ba, ka bar Hadiza taje ta yi aure a waje. Jibi ne dai tafiyarku Allah ya tsare muku hanya. Kaga sai ka roƙi Allah in wannan kujera alkhairi ce Allah ya baka, in ba alkhairi bace Allah ya maye maka gurbinta da wani babban rabon tashi ka tafi Allah yayi albarka." Tafiya Gwadabe yayi shi ba wai son zama da Hadiza yake yi ba, a_a kunyar Malam da su Mammada yake ji kawai. Bayan kwana biyu jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasa mai tsarki. Malam ya shiga gidan ya tadda Hadiza tayi tagumi ta zurfafa a cikin tunani. Abinka da mahaifi sai yaji zuchiyarshi ta karaya. Kuma kaza tana taka ɗanta ne ba dan bata so ba. A ranshi yake hangoma Hadiza irin asarar miji da tayi dan Gwadabe guda da ɓari ne. Hadiza ta ɗago suka haɗa ido da Malam tace. "Sannu da zuwa Malam " Ko kallonta bai kuma yi ba balle ta saka ranta zai amsa mata. Tunda abun ya faru kowa ya juya mata baya a wajen Baba Asshi kawai take jin sanyi. Kullum sai ta gwada mata illar kishi mai zafi. Sabitu kuwa duk shigowa sai ya zunguri kan Hadiza kafin ya fita. Ta rame duk ta lalace decoration kuwa ƙaƙas. To bari in numfasa a han sai jibi kuma in Allah ya kai rayuwarmu. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUDU (8) TABALBALIN" Da duk naci irin na Hafizu a bisa tilas ya sararama Uwani dolenshi, musamman daya lura kamar kuttun farin jini ya fashe mata. A wata huɗu da rabuwarsu Uwani ta sake gogewa ta zama cikakkiyar babbar mace, dan da kanta yanzu take zuwa makka siyayyarta bata tsayawa jiran komai. Allah cikin ikonshi a irin wannan tafiye_tafiyen a cikin jirgi Allah ya haɗata da Alhaji Sama'illa. Hamshaƙin ɗan kasuwane dattijo ɗan gaye. Allah ya daidaita tsakaninshi da Uwani kamar dai wasa suka ƙulla mu'amular soyayya tare da alƙawarin aure bugu da ƙari. Muddin Uwani na gari to Alhaji Sama'ila baya rabo da kawo ma Uwani ziyara barenma da yasan ya miƙa sadakinshi gidansu Uwani an tsayar da lokacin aure. Wata ranar laraba Hajiya Uwani tana shagonta tana jera kayayyakin data saro, yaran shago na ta aikinsu, ta faɗaɗa shagon nata an ƙara ƙawatashi ga kaya danƙan. Sai ga Hafizu da yaranta sun shigo. Kallonsu tayi taci gaba da aikin da take yi har saida ta gama ta dubi babbar ƴar tace. "Ummu Kursum lafiya na ganku anan ina makarantar fa? Carab Hafizu yace. "Wallahi Hajiya korosu akayi Uwani, ni kuma a yanzu bani da kuɗin dazan biya musu kuɗin makarantar shine nace musu su zo mu zo mu sameki ko bashine a bani in sha Allah dana dawo daga tafiya zan dawo miki dashi" Uwani ta dubeshi ta sake dubanshi ta dubi yaran duk dai ita suke kallo sai ta haɗiye duk jarabarta. Ana cikin haka kuwa sai ga Alhaji Sama'ila ya parka motarshi a gefen shagon Uwani. Fitowa yayi yaci uwar kwalliya sai ƙamshi yake busawa ya shiga shagon ya nemi waje ya zauna. Hannu ya miƙa ma Hafizu suka gaisa. Dama dai sun san junansu a shagon uwani, kuma Hafizu yasan shi zai auri Uwani "To ku taso anjima ma dawo umma tayi baƙo ko Ummu Kursum" Cewar Hafizu yaran suka gaishe da Alhaji Sama'ila ya amsa da fara,arshi dama ya sansu suna yawan zuwa wajen Uwani cin abinci. Kuɗi ya ciro masu kaurin da zai isa a biya musu kuɗin makarantar ma ya basu. Hafizu ya kama hannunsu suka fice, kai tsaye ya mayar dasu makaranta. Da wannan kuɗin ya biya kuɗin makarantar ragowar kuma yayi cefane ya nufi gida bagazan_,bagazan "Ranki shidaɗe kina ta jera kaya a shago. Ni na faɗa miki wannan shagon kasuwa zai koma can idon mutane. Na yi tunanin tunda dai bikin namu baifi wata ɗaya ba nayi tunanin ma ba zaki buɗe dilar ba har sai an samu shago uhm?" Murmusawa tayi tace. "Ai da ni nayi tunanin wannan ɗin in barshi aci gaba da kasuwancin tunda dai an saba kuma ana samun ciniki ko su ummi sa dinga lurarmun dashi. Sai a sake buɗe sabo a kasuwar ma." Idanu ya zuba mata yana murmushi yace. "Hakan ma wata dabarar kasuwanci ne. Amman kina da kuɗin da zai isheki saro kayan da zaki cika shi shagon na kasuwarne da girma shagunan kasuwa?" Dariya tayi yace. "Za'a gagganɗa ayi abinda ya dace, ko dila biyune zan harhaɗa kuɗin harda na aminiyata in saro kayan in yaso na dinga cire mata riba. Kuɗaɗen hayar gidanta suna nan jingim a hannuna. Allah sarki Iyabo alkhairin Allah ya kai miki a duk inda kike haƙiƙa munyi babban rashi, ko in mijin baiwar Allahn nan ya dawo ya zai ɗauki wannan babban lamari sai Allah" Ajjiyar zuchiya ta sauke ta shiga damuwa lokaci guda harda hawayenta. Alhaji Sama'ila ya shiga aikin rarrashinta. "Gaskiya akwai shaƙuwa mai ƙarfi tsakaninki da Iyabo a haɗuwata dake na fahimci hakan tun kafin ki bani labari a kanta. Fatanmu shine Allah yasa ta faɗa hannu na gari. Allah ya dawo da'ita cikin ahalinta shine. "Ameen Ameen." "To ni batun kayan lefe ne ya kawo ni ma Shin kuɗin kike da buƙata, ko kuwa a haɗo akwatunan wanne kika ga yafi?" Ɗan murmushi tayi tace. "Zan fi buƙatar kuɗin gaskiya. Suturu kam Alhamdulillah a cikin ɗinkasu ake. Akwai abubbuwan da ban ƙarashe ba na kayan ɗaki to kuɗin zai taimaka sosai" "To Shikenan dubu ɗari biyu yayi miki?" Ya tambaya yana kafeta da idanunshi. "Sunyi sosai ma, nagode sosai Allah dai ya tabbatar da Alkhairin shi. Sannu da ɗawainiya." Hira dai suka taɓa kafin yayi mata sallama shi kam zai tafi zuwa gobe zaije banki ya ciro mata kuɗaɗen a haka suka rabu. Dubu ɗari biyun da mai daraja fa ba irin ta yanzu ba ehe. Washegari kuwa kamar yadda yayi alƙawari sai gashi da wannan kuɗi. Uwani ta harhaɗa da kuɗaɗenta tai ma kanta kayayyakin ɗaki na fitar raini. Kayayyakin kitchen kuwa dama daga saudiyya duk ta siyo abunta. Turarukan wuta kuwa show glass guda Uwani ta siya a wajen Mrs Bukhari gidan ƙamshi ( Ina iyayen amare, ina amaren, da zauwara ina haɗa turarukan wuta na amare na musamman har show glass duk ina siyarwa mai cike da kwalabe da turarukan wuta da humrori kala_kala. A sauƙaƙe inayin adashe domin samama iyayen yara sauƙi sai ki zuba kuɗin a hankali kafin zuwan lokacin biki aikinku ya kammala da izinin Allah. Iyayen gida ma inayi muku taku show glass ɗin ta turaruka da humrori domin burge mazajenku, ki sani ba Amarya bace kaɗai take da buƙatar show glass ta turaren wuta ba kema kina da buƙata) Uwani ita taima kanta komai da komai. Ta samu manyan kaya kala goma ta ɗinkesu. Ana biki saura sati biyu Alhaji Sama'ila ya kirata yake sanar mata an samu wani danƙareren shago mai ƙofa biyu a kasuwa ya kama mata. Sauran ya rage nata zuba kaya da buga kantoci. A wannan karon haɗa kuɗaɗen tayi ta tura ma Faty, ragowar kuɗaɗen hannunta ta biya masu buga kanta suka soma aikinsu. Sati biyu na zagayowa fa aka ɗaura auren Uwani da Alhaji Sama'ila. Da daddare aka raka amarya gidanta dake unguwa uku. Falon uwargidan Alhaji Sama'ila cike da ƴan uwanshi da ƴan uwanta aka shigo da Amarya idanta a buɗe fes babu wanda ya ma riƙeta. "To ga Amarya mun kawo miki Hajiya Mansa. Sai ayi haƙuri da juna dan Allah a zauna lafiya" Cewar yayar Hajiyan Uwani kenan. Hajiya Mansa tace. "Allah ya bamu zaman lafiya. Ubangiji Allah yasa da Alkhairi ta shigo. Ɗakin Hajiya Sa'a yana sama in kun haura kusa da ɗakin Amaryar." "To mun gode ƙwarai Allah ya haɗe kawunanku baki ɗaya" Nan ƴan rakiyar Uwani suka fita daga ɓarayin uwargida sarautar gida. Zuwa ɓangaren da yake gidan sama mai hawa biyu. Hawan farko anan ɗakin Uwani da ɗakin Hajiya Sa'a yake. Saman kuma turakar ogan da kanshi ne. Gidan fa akwai girma arziki da gani ya zauna da ƙafafunshi. Hajiya Sa'a ma babu laifi ta tarbi su Uwani babu yabo babu fallasa sai dai ba kamar yadda Hajiya Mansa tayi musu ba. Falukan gidan danƙama_danƙamane ko wacce ɗakinta cike da kayan alatu. Ajjiyar zuchiya Uwani ta sauke data shiga nata falon taga babu raini, ga wasu irin manyan frames dake mammanne a bango da suka ƙara ma falon kyau da tsari. Ƴan rakiyar Amarya basu daɗe ba sukai ma Uwani sallama su ka yi gaba. To ita ba yarinya ba, bayan ta gama zagaye ɗakunan nata sai ta dawo ta zauna a falo ta kunna tv. "Oh Allah mai iko ni Uwani yau nice a cikin irin wannan daular, a tsakankanin hamshaƙan mata masu ji da kuɗi da kyau? Iko sai Allah wallahi Allah kuɗi yayi a rayuwa. Ya Allah ka baiwa yaranmu mazaje masu rufin asiri suje su huta suma. Ya Allah ka kaɗe fitina a wannan auren Allah kana ganin irin azabar da Hafizu ya dinga gana mun Allah kasa Alhaji Sama'ila ya riƙe ni da kyau" Sallama ta jiyo daga bakin ƙofar falon nata. Ta taso da yanga ta buɗe. Hajiya Sa'a ce tafe da ƴar aiki hannun ƴar aikin ɗauke da ƙaton tire jere da wasu kuloli na alfarma. Tace. "Amarya ga abincinku nan ke da Alhaji. Wannan sunanta Laure ita ke taya mu aikin girki. Laure shiga ki jera mata in tana da daining in babu kuma ki jera mata a ƙasa" Tana idasa faɗe ta juya. Waje Uwani ta ba Laure ta shiga ciki ita kuma tana tsaye tana murmushi magana ce nan Hajiya Sa'a ta mugun yaɓa mata. Bata sam waye Uwani bane shi yasa. Ta lura da yanayinta dama. Kuma ko suna tare da Alhaji Sama'ila Hajiya Sa'a tafi yawan kiranshi a waya. Hajiya Mansa sau ɗaya tak ta taɓa kiranshi suna tare. Kenan dai Hajiya Sa'a itace ta gaban goshin Alhaji Sama'ila tunda itace Amarya kuma ba wata babba bace itan bata wuce shekarun uwanin ba. Saɓanin Hajiya Mansa da take dattijuwa mai samari da ƴan matan ƴaƴa. Laure ta gama jera kayan abincin a kafet ta fita. Uwani ta dawo ta zauna. Sai kuma ta tuna ai ya kamata ta kunna burner ta saka turaren wuta. Ai kuwa haka akayi ta harhaɗa turarukan wuta kusan kala goma ta kunna a bona ɗakin take ya karaɗe da wani sassanyan ƙamshi na kece raini. ( Akwai mix turaren wuta wanda ya haɗa duk itacen turarena fin kala goma a cikin kwalba ɗaya. Wannan wani babban sirrine na musamman wanda in kika riƙe duk ƙwaƙwar mai ƙwaƙwa bai isa ya gano da wanne itacen turare kike amfani ba. Yananan a babbar kwalba mai cin 1 litter haka na zuzzubasu. Siyan jagari) Alhaji Sama'ila ne ya kwankwasa ƙofar yana ƙwala kiran honey " Murmushi Uwani tayi ta daka tsallen murnar wai yau itace da miji mai kuɗi miji wayayye ɗan gaye har yake kiranta da Honey. Sannu a hankali ta isa bakin ƙofar ta buɗe mishi. Tayi saurin amsar ledojin hannunshi ta shigar dashi. Ɗakin yake ta ƙarema kallo yana yaba kyau da tsarin ɗakin" "Ɗaki yayi kyau mai ɗakinma tayi kyau. Saura abu ɗaya ya rage miki gobe in sha Allah zansa a kawo." To daga haka dai aka ci kaza akayi Sallah. To mai ya rage kuma? Na baku gari ku fasalta wannan dare a ƙwaƙwalenku. Washegari Amarya ta tashi da farin cikin shiga sabuwar rayuwa. Angoma ba'a barshi a baya ba. Amarya dai amaryace ko da kuwa ta buzuzuce. Balle Uwani zagewa tayi ta gyara jikinta ƙaƙas. Kuma da ingantattun kayan matan Ramlex kwamishiniyar buje tayi amfani. Bayan ya dawo masallacine yake sanarma Uwani. "Yaufa abincin Amarya zamu ci" Da mamaki Uwani tace. "Amman dai wasa kake yi ko? Yanzu duk wannan kwalliyar dana rangaɗa sai in shiga kitchen?" Idanunshi ya lumshe yana ci gaba da shaƙar humrar matan auren da uwani ta shafa yake fisgarshi. "To kiyi haƙuri ba haka naso ba, amman kinsan sha'anin kishin mata. Ita Hajiya Mansa ma bata nan suna da biki a family House ɗinsu ita da yaranta kab sun tafi. So abincin ba mai yawa zaki yi ba. Nawa da naki ne saina Sa'a da yaranta. Sai na masu gadi" Murmushi Uwani tayi, ta saki hannunshi ta miƙe. Mayafi ta yafa daidai da kalar kayanta. Da ciro sabon takalmi ta saka ta gangara ƙasa acan babban kitchen ɗin gidan yake tangamemen gaske. A kitchen ɗin ta tadda Laure tana jiranta. "Hajiya barka da fitowa" "Yauwa Laure. To in akwai doya ki fere mun dan Allah, ina fatan ban makara ba dai ko?" Ta ƙarashe maganar tana dariya. Laure ma tayi Dariya tace.. "Baki makara ba dake yaran anyi musu hutun boko, islamiyya kuma sai ƙarfe goma suke tafiya. Nan dai Laure ta taimaka ma Uwani ta soya doya, ta yi miyar ƙwai kana ta dafa tea. Laure ce ta nuna mata durowar da kayanta suke ciki, ta kuma sanar mata ai ko kulolin abincin jiya nata ne a durowarta Hajiya Sa'a ta ciro aka zuba mata abinci a ciki. Nan dai ta nuna ma uwani yadda suke yi. Godiya tayi mata sai wajen taran safe suka gama kammala komai. Uwani ta haɗa nasu a babban tire. Laure ta haɗama Hajiya Sa'a nata. Haka da rana ma Uwani ta fito ta yi girki a lokacin oga ya fita har ya turo mota da daining table mai kujeru shidda an saka ma uwani. Da daddare Uwani tuwo tayi musu miyar ganye taji bushasshen kifi da naman kaza tayi musu jus na kankana. Kafin ƙarfe biyar ma ta sallami kowa ta shalla wankanta ta buɗe ɗakinta da turarukan wutanta tana jiran mijinta ya dawo. A haka har Uwani dai ta cinye kwana ukunta Hajiya Mansa bata dawo ba. Yau sa'a ce da girki Uwani tana kwance tana kallo a tashar zee aflam tana shan jus sai ta jiyo sallamar su ummi sun rako Hajiya ganin waje. "Uwani yau kece a cikin irin wannan duniyar? Allah da iko yake." Hajiya ta shiga kalle_kalle. Uwani tace. "Hajiya ku zauna dai. Bari in sanar ma da Laure zuwanku a haɗo muku abinci. Ina zuwanku. Sauka tayi har zuwa kitchen ɗin gidan. Hajiya Sa'a na ciki Laure na kama mata girki tace. "Hajiya Sa'a barka dai da aiki" Juyowa tayi ta zuba ma Uwani idanu kafin dai ta danne abinda ya taso mata tace. "Yauwa Hajiya Uwani." "Dama Hajiyata ce tazo shine nace bari in sanar muku a saka sanwa dasu" Murmushi tayi tace. "Ayya sai dai ki shigo ki ɗaura musu kinga harna gama girkin dama yanzu Laure zata miƙa miki naki. Nan gaba kya sanar da wuri in zaki yi baƙi ko?" Sai ta juya tana rufe manyan kulolin Oga da za'a kai mishi abinci kasuwa. Murmusawa Uwani tayi ta koma sama. Ruwa da lemuka ta dure ma su Hajiya ta shige ciki ta kira Alhaji ta sanar mishi yadda suka yi da Hajiya Sa'a cikin hikima. Dan tayi ne kamar tana bashi labarin ai girki ma zata sauka taje tayi musu Hajiya Sa'a ta riga ta gama aikin rana. Yayi maza yace. "A_a bari in kirata aba su Hajiyan nawa. Mu ko taliyane ta sake ɓararraka mana. Ina zuwa" Murmusawa Uwani tayi tace. "To Shikenan Alhaji babu damuwa godiya nake" Ya aka ƙare oho dai dole ƙanwar naƙi aka hauro ma da su Hajiya abincin Alhaji. Suka zauna suka kwashi gara. Sai dab la'asar Hajiya tace su ummi su taso su tafi. Har ɗakin Hajiya Sa'a Uwani ta kai Hajiya. Ta tarbeta da kyau babu laifi ta ɗanyi musu nasiha dai haka kafin uwani ta rakosu bakin get. "Gashi Hajiya wannan kuyi na mota. Saina shigo nima. Ummi a kula dai da shagon dan Allah" Nan su kai sallama Uwani ta koma sama abinta. Ana idar da sallah sai ga Alhaji ya shigo. Ya samu Uwani na shan fura ai sai ya gyara zama aka shanye furarnan dashi, suka dai ɗan taɓa hira kafin yayi mata sallama. Ranar da Hajiya Sa'a ta fita a girki, a ranar Hajiya babba ta dawo cikin gidan da ƴaƴanta ta amshi girki tayi. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU (9) IYABO:. Mayafina na saka na fita cikin nutsuwa. Yana cikin mota idanunshi ƙur a ƙofar gidanmu. Wannan karon fararen kayane a jikinshi ɗinkin malum_malum, da hularshi ƴar asali zanna bukar, kunsan akwai zanna habu. Ganin yaƙi fitowa yasa na zagayo na shiga motar Juyowa yayi da kyau yana ƙaremun kallo yana murmushi. "Gimbiya ji nake kamar in tada motarnan in wuce dake gidana duniya ta dena kallemun ke. Babban abinda yafi komai farin ciki shine Alhajina ya bani goyon bayan ƙarin aure ɗari bisa ɗari. Yanzu abinda kawai ya rage shine dana dawo ayi batun aurenmu." Murmushi kawai nake ta yi nutsuwarshi na burgeni sosai. To Alhamdulillah. Da Farko dai ya hanya, ina fatan ka iso lafiya ko?" Idanu ya lumshe sosai kana yaace "Lafiya lau na iso gimbiyata. Ya soyayyata da fatan dai kina killace mun kanki ko?" Sosai ma ai ba kai kaɗai son yai ma kamu ba harda zuchiyar Iyabo. Yanzu dai mu shiga daga ciki ka samu kaci abinci tukunna" Saida ya gama ƙaremun kallo kana yace. "To Shikenan muje. Bari in kashe motar aro" Dariya mu ka yi dukkanmu ya zare keyn motar muka fito. Ledoji ya ciro a bayan both muka shiga gidan tare. Ƴan matan gidan duk suna tsakar gida sabida tsabaragen gulma. Har suna haɗa baki wajen gaisheshi. Ni dai na shige dashi zuwa ciki ya zauna a shinfiɗar da nayi mishi yanata kallona. "Kinsan menene gani nake yi da Alhaji zai mun alfarma da an ɗaura aurennan kafin in koma wajen aikina kinga sai mu koma tare ko?" Ƙarashe zuba mishi abincin nayi na turo gabanshi na nemi waje na zauna. Ba a Gomben kake aiki bane daman?" "Nayi babban laifi ban sanar dake ba ko? A India nake aiki a wani asibitin mahaukata. Inna tafi wata huɗu nake yi kafin in dawo. Amman ina tafiya da mace ɗaya in zan dawo sai in dawo da'ita in ɗauki wacce na bari haka muke yi. Amman ke kam acan zaki zauna tare dani, ba na son ki tambayi dalili kuma" Murmushi nayi a zuchiyata ina ta jujjuya lamarin dai. Yana cikin cin abinci sai ga Batula ta shigo da biyu a hannunta. Suna ganina suka soma zullo. Ƙur yayi musu da fararen idanunshi irin nasu. Hannu ya miƙa Batula ta bashi Usaini. Ni kuma ta ajjiye mun Hassan ɗin. "Barka da zuwa master da fatan ka iso lafiya?" Dariya yayi yace. "A ina na samo suna master ni Usman ɗan Usman?" Batula tace "Master a zuchiyar maman biyu mana. Gaskiya dai kaci sa'a ka warce zuchiyar Iyabo " Kallona yayi yace. "Wai hakane gimbiya abinda ƙawarki tace?" Sosai kuwa abinda ta faɗa hakane" Da dariya da wasa suka gaisa tayi ficewarta. Sai ya bar cin abincin ya shiga wasa da ƴan biyu. "Dr ya fa kamata ka bar yarannan kaci abincinka kar yayi sanyi ko? Kaga kawo shi. Nayi yinƙurin ɗauke Usaini a jikinshi ya hanani fur daga ƙarshe ma yana cin abincin yana basu suna ci. Ni kuma sai nake musu kallon sha'awa. "Kin yi shiru kina ta kallonmu ba dai tunanin tsohon mijinki kike yi ba dai ko? Yaji shiru na zurfafa tunanin da in wuƙa za'a saka mun ni bansan tunanin me nake yi ba. "Gimbiya kina tare dani?" Ya faɗa da ɗan ƙarfi kafin naji me yace na yi saurin kallonshi, sai yaga hawaye fal idanuna. Ƙuramun idanu yayi sosai yana kallona har hawayennan yabar guraben idanuna ya shiga sauka a kumatuna bai dena kallona ba. Da dai yaga kukan yaƙi ci yaƙi cinyewa sai ya lumshe idanunshi ya sake buɗesu a kaina. "Iyabo kamar Baban yarannan yana zuchiyarki kenan fa. Duk da dai dama nima nayi karambanin shigewa rayuwarki, da ma zurfafa akan sonki ba tare da naji tarihinki da asalin abinda ya fito dake ba. Duk da dai Hajja Mama ta faɗamun ke ƴar uwarta ce ta jini aurenki ne daya mutu tasa aka kawoki wajenta shi ya bani ƙarfin guiwa. Zan barki kiyi tunani ki zaɓi abinda yafi miki kyau ni ko tsohon mijinki' Yana dasa aya ya miƙe tsaye hannu yasa a aljihu ya zaro kuɗi ya ajjiyesu a gabana. "Zuwa jibi zamu koma India sai nan da wata huɗu zan shigo najeriya na barki lafiya" Ya saka kai ya wuce. Har ya fita ban iya motsawa ba bansan kukan me nake yi ba gaskiya. Da sauri na miƙe na fice a gidan yana cikin motarshi ya ɗaura kanshi akan sitiyari na buɗe murfin motar na shigo. Baiko ɗago ba idanunshi ma a rufe suke yanata dai karanto adda'a" Wallahi ina sonka so na gaskiya. Karma shaiɗan yayi tasarin rabamu. Batun uban ƴaƴana babu a raina ka yarda dani." "To menene silar zuban hawayenki da har kike ƙoƙarin tayar mun da ciwona uhm?" Wallahi da kai da yaranne kuka bani sha'awa wannan shine silar zubar da hawayena" Ajjiyar zuchiya ya sauke mai nauyi sai lokacin ya ɗago kanshi ya zuba mun idanunshi har sun sauya nauni. "Wai ke kinji irin luguden da zuchiyata take yi kuwa? Ji nayi inna rasaki komai zai iya faruwa dani. Kinsan ni ban iya son abuba Alhajina kullum a cikin yi mun nasiha yake sabida a gaskiya so ya bani wahala sosai bazan ɓoye miki ba" Kafin kayi auren fari kenan ko bayan kayi?" Dariya yayi sosai tare da duba agogon hannunshi. "Ki shiga gida gimbiya zanje hotel in ɗan watsa ruwa in kwanta kaina ma ciwo yake yi kece kuma sila" Hannuna na haɗe waje guda nace. Tuba nake yi ranka shi daɗe aimun afuwa dan Allah. Kaje Allah ya huce gajiya sai yaushe kuma?" Idanu ya lumshe yace. "Sai dare in nazo sallama dake gobe da sassafe zan juya, jibi zamu bar ƙasar kinga Suhaila na buƙatata a kusa da'ita ko?" Ya ƙarashe maganar yana mun dariya. Hakane kam tana buƙatarka. "Kafin in dawo zan turo iyayena ayi komai a gama nan da wata biyu in an ɗaura auren zanyi ƙoƙari in dawo sai in tafi dake kudun kallon ruwa kwaɗo yazo yai mun ƙafa. Amman me kike gani? Bari in nazo da daddare zamu tsaida magana " Da haka mu kai sallama ya tafi. Na dawo na tadda Batula a gaban kayan tanata dubawa kayan tea ne manya manyan gongoni, sai atampa da bayafai da wani turare mai ruwan ja a jikinshi. "Zaki fita ki bar damin kuɗi a yashe sabida rashin hankali?" Ke dai bari ana ta kai wama yake ta kaya. Ke Batula gayennan fa aure yake so muyi faka_faka nan da wata biyu. Ni babbar damuwata shine abubbuwan dana manta na baya. Bazan iya ce miki wacece ni ba wallahi, babu abinda zan iya tunowa" Ajjiyar zuchiya Batula ta sauke tare da dafa ni tace. "Al'amarinki da girma kuma akwai sarƙaƙiya sosai. Amman ni ina ganin kar ki rufi Usman ki faɗa mishi gaskiya amman ki bari ayi auren tukunna gudun kar ki faɗa mishi yanzu yazo ya fasa ko iyayenshi su kawo cikas. Hajja Mama ta riga data sanar mishi ke ƴar ƙanwarta ce. Ta aurar da mata da dama ba tare da sanin danginsu ba dan wasu ma musulunta su ka yi, kuma suna zaune wasunsu a gidan miji. Ni ina ganin karma ki damu muyi ta shirye_shiryen biki kawai kefa kakarki ce ta yanke saƙa wallahi. Dariya mu ka yi harda tafawa. Zuwa bayan isha sai ga kiran Usman bin Usman ya zo yana ƙofar gida. Dama na yi kwalliyata nayi kyau shi kawai nake jira, motar na ɓalle na shiga, wannan karon wankan ƙananan kaya yayi sai yayi yaro dashi. Motar kawai naga ya ja mun hau titi. Ina zamu je ne?" "Kina tsoron kar in sace ki ko?" Dariya mu ka yi duka kafin yace mun wani ɗan waje zamu je mu zauna inda zamu samu nutsuwa da damar gabatar da abinda ya kamata na dangane da bikinmu Wani ɗan gidan abinci ya kaimu muka zauna odar abun sha kawai yayi mana. "To ina jinki me kike ganin ya dace ki tsara ta ɓangarenki? Zasu kawo lefe da sadaki, me kike so daga gareni kuma? Dan har nayi ma Yata magana ta haɗa mun lefe gangariya." Ni dai jikina a mace tiɓis sai nake jin wani raɗaɗi a zuchiyata wanda bansan na menene ba. To ni dai lokacin ne nake tunanin yayi wuri me zai hana a barshi a wata huɗun kafinnan na kammala shirye_shiryena a hankali? " Sai ya haɗe ranshi, ni kuma zuchiyata sai lugude take yi mini. "Wanne irin shirine wannan da ba za'a iya yinshi a wata biyun ba to? Mu da ba yara bane da zamu yi ta yin taɗi ba." Da ƙyar nake danne wani abu dake hankaɗo kanshi a zuchiyata. Kayan ɗaki, da dai abubuwan da ba'a rasaba namu na mata" Dariya yayi mun yace. "Zamu yi magana da Hajja Mama duk abinda ake buƙata zanyi daidai gwargwado. Ni fa ke kaɗai nake buƙata barinma data faɗa mun ke marainiyace ashe mahaifanki duk Allah yayi musu rasuwane. Allah ya jiƙansu da rahama in sha Allah ni zan maye miki gurbinsu" Ameen to nagode" Iyakar abinda na iya cewa kenan kawai sai na ɓalle da kuka kukan da ni bansan na menene ba rayuwata ce naji tayi ƙunci sosai. Shi kuma rarrashina ya dinga yi yana tunanin sabida mahaifanane dana tuna. Haka dai mu kai sallama babu daɗi. Washegari sassafe jirginshi ya ɗaga. Hajja Mama ce ta zaunar dani take mun gargaɗin ko da wasa kar in kuskura in nuna mishi manta rayuwata ta baya nayi in ba haka ba bazai taɓa auren marar asali ba. In barshi a zuwan iyayenane suka rasu in rayu cikin daula in mance da damuwar komai. Ita a tunaninta tsabar azabar da rijalu ƙila suka ganamunne yasa ƙwaƙwalwata ta samu matsala. Bata san al'amarin nawa babba bane ga dai aure a kan aure yanata tunkarowa. A kullum shaƙuwar dake tsakanina da Usman sai sake yaɗuwa take yi, sai na shiga tunanin san tuna wacece ni sai inji rayuwata tayi ƙunci kai wata shari'ar sai a lahira akan wata cutarwar da za'ayi maka. Kamar yadda Usman ya faɗa ya tafi da wata guda aka kawo lefena garin Lagos wajen Hajja Mama. Dangin arziki ne Usman sosai dan ƴan uwanshi sun kasa ɓoye mamakinsu akan irin gidan da yaga yarinya yake son Aure. Yayar Usman Anty Sumayya ce ta buƙaci ganina Hajja Mama tasa aka kawota ɗakin maƙotanmu dana je na ɓoye kaina ina risgar kuka. Shigowarta yasa nayi shiru Tayi matuƙar kama sosai da Usman dake ita macece harta fishi haske. Ina ganinta na gane itace cikin girmamawa muka gaisa harma ta kira Usman ɗin take faɗa mishi ai kuka ma ta taddani inayi dai haka. A ranar suka bi jirgi suka koma Gombe akan ɗaurin aure a Kontagora za'aje ayi can asalin gidan iyayen Hajja Mama. Ta nunar musu can ne family House ɗinmu. Haka dai mukaita shirye_shirye Usman ya turo ma Hajja Mama wadatattun kuɗi akan ta sai mun kayan ɗakina masha Allah, bata siya ba tace mun in muka je Gombe ma siya acan a jera mun komai. A cikin lefennan na dinka kusan rabin kayan dan Usman yace yana dawowa kwana uku zaiyi mu koma India, kunji fa wata ƙudurar Ubangiji. In aka kaini Gombe Anty Sumayya zata kaini aimun paspo. To kar ku mance na taɓa yin paspo a baya fa. Ranar juma'a aka ɗaura aurena da Usman a Kontagora gidan su Hajja Mama. Muma duk can muka ɗunguma muka tafi dan ana ɗaura aure zasu jiya da Amarya dalilin da yasa aka tawo da mata kenan ƙannen mahaifin Usman. Ina ɗaki kaina na mun wani irin ciwo kamar zai tsage, ga wani irin faɗuwar gaba dake damuna. Ni a tunanina yana da nasaba da aurena da aka ɗaura sai ga kiran Usman ya shigo wayata. Da ƙyar na ɗauka dan jikina har rawa yake yi na kara wayar a kunnena. Sai na fashe mishi da kuka kawai. "A_a Gimbiya kar ki karya mun zuchiya kisa inyi tunanin ba sona kike yi ba mana. Kiyi shiru kinji ko? Yanzu za'a kai mun ke gidana a matsayin mallakina. In sha Allah zan tallafi duk maraicinki da rashin gatanki. Daga yau kin zama mai gata. Ki nutsu ki mana adda'ar samun dukkan alkhairai ina dawowa zamu tafi zaku je ayi miki paspo ke da Anty Sumayya zata rakaki. Nan ma sai faman rarrashi nake yi, itama Suhaila inata fama duk da dai nata da sauƙi. Kiyi shiru ki tashi kisa kaya masu kyau kar ki bari dangina da dangin abokan zamanki su raina shigarki uhm?" Ajjiyar zuchiya na sauke nace. To Shikenan zanyi yadda kace nagode sosai da kulawa. Ina fatan ka kula da rayuwarmu sannan Allah ya bamu zaman lafiya da fahimta a tsakanmu baki ɗaya mu huɗun" "To Ameen. Daɗina dake kin iya sarrafa harshe kamar wata marubuciya. Allah yayi albarka" Da haka mu kai sallama sai naji dama_dama a jikin nawa. Hajja Mama ce ta shigo mun da kayan da zan saka wani farin lace ne fari tas mai tsadar gaske, da takalmi da jakata suma na gasken, da mayafina duka farare. Dama sarƙa da ɗan kunne dake wuyana silver ne. "Saka kaya maza mu je ashe a jirgi zamu je mu bamu sani ba. Goggona da ƙanwata su ne zasu kaiki a matsayin iyaye. Iyabo kiyi ƙoƙarin birne wannan sirrin dan Allah. Kinsan Allah bayyanuwar rashin asalinku barazanane babba. Kinga famaly babba kika shiga kuma mijinki na da ƙanne maza duk masu aure ne. Saka maza ki fito" Saya kayannan nayi Hauwa ta sake gyara mun kwalliyata na fito shar dani kunsan masu ƙiba ba yabon kai ba kwalliya da ado yafi karɓarsu, gashi na sha ƙunshi ja da baƙi, ga kitso ƙananu irinna matan kanuri an yarfa mun. Ƴan biyu na wajen su Hauwa muka fito, sai shatar motoci aka ɗauka zuwa filin jirgi. Misalin biyu na rana jirginmu ya ɗaga zuwa Gombe ƙarfe 3 da minti goma muka sauka a filin jirgin Gombe motoci daga ɓangaren ango suna waje suna jiran Amarya. Ni dai ni da Hauwa da yarana muna bayan wata ƙatuwar mota sai ajjiyar zuchiya kawai nake sauke wa, da kuma hawayen da ke sakko mun lokaci zuwa lokaci har muka iso cikin unguwar fediral kwatas a wani katafaren gida motocinmu suka tsaya. Ni dai sai ƙare ma unguwannin kallo nake yi ina mamaki har muka shiga cikin gidan mai yalwar tsakar gida. Dangin Usman ne cike da gidan ashe nan gidan mahaifinshi ne ba can gidan shi ba. Ɗaki aka bamu sukutum mu da su Hajja Mama akan zuwa gobe kuma sai su shiga kasuwa su siya mun kayan ɗaki. Dangin Usman sun karramani sosai, sai tururuwar zuwa ganina ni da ƴan biyu suke ta yi, daga ƙarshe ma ficewa akayi da ƴan biyu zuwa can ɓarayin Alhaji Baba kamar yadda suke kiranshi. Lokacin ne na samu na ɗauro alwala a ban ɗakin cikin ɗakin na yi Sallah. Ina idarwa sai ga kiran Usman ya shigo wayata. "Gimbiya barka da shigowa Family na. Kiyi haƙuri kinga an wuto dake family House ko? Alhaji ne yace sai dai ku sauka a ɓarayinshi abinda bai taɓa yima wata suruka ta gidan ba kenan. Yanzu dai ki sake sauya kaya zaku fita da Anty Sumayya yanzu batun paspo." To Shikenan muna godiya da wannan karramawar Allah ya saka da Alkhairi" "Ameen daɗina dake abinda bai taka kara ya karya ba sai kiyi ta godiya da shi albarka" Hirarmu dai ba ta yi nisa ba muka ajjiye wayar. Da zallan soyayyun kaji da aka tsoma a jajjagen attaruhu da albasa aka tarbemu da jus na kwali masu daɗi gaske na gwaiba sai daga gidan uwargidan Usman aka aiko tuwon sakwara da miyar egusi lafiyayyen gaske. Ni bamma ci abincin ba wanka kawai nayi na sake kayana muka fita ni da Anty Sumayya a mota har zuwa ofishin paspo. "Hajiya menene sunanki, sannan shekarunki nawa" Sunana Iyabo." Tofa kafin ya gama rubuta sunan sai ya dubeni yace "Iyabo Adetoye? Ai kin taɓa yin paspo ɓata yayine?" Shiru nayi ina zare idanu a ƙoƙarina na son tunawa. Kafin in yi magana Anty Sumayya tace. "Tunda kaga munzo kuma tasan ta taɓa yi ƙila ta rasashi ne a bamu sabo kawai. Ko Iyabo?" Ta yi maganar tana murmushi nima murmushin nayi mata wanda bai kai ciki ba. Inata tunani da ƙoƙarin ko zan tuno ɗan wani abun ko da babu dai yawa. Wannan ma'aikaci yace. "Babbar Yaya gobe zan kawo muku in sha Allah har gida kuje kawai. Ai da munsan ta taɓa yi ma da ba sai kunzo ba suna kawai zata faɗamun" Sallama mu ka yi mishi muka koma gida. A babban falon gidan muka tarar da Alhaji Baba ya sakko daga sama da matarshi surukanshi sun zagayeshi da jikoki. Fari kyakkyawan namiji mai cikar haiba. A gabanshi na durƙusa na gaisheshi. Ya amsa mun da fara'a tare da shi mun albarka. Da kanshi ya dinga nuna mun matan ƙannen Usman. Mazajen nasu daga lauya, sai ɗan siyasa, sai likita gasunan dai gwanin ban sha'awa. Matan kuwa tamkar zaɓosu akayi dan kyau. Ko wacce da gani tana ji da asali da dukiya. Ai saima na raina kaina ƙibatace kaɗai ta ɗan ceceni ma na cika musu idanu. "To kuje na sallameku zanje masallaci. Sumayya abar Iyabo ta Zauna har zuwa lokacin da Fodiyo zai dawo. Munyi waya dashi ɗazu yake sanarmun bazai samu tasowa jibinnan ba sai sati mai zuwa. To ta zauna kawai in yazo ya ɗauki matarshi su wuce daga gidannan. Ko kuwa Hajiya Iya?" Matarshi kenan. Amman ba ita ta haifi kusan manyan gidan ba, ƴaƴanta sune ƙanana a gidan. Amman a halin yanzu itace kaɗai a wajen mijin nata. "Hakan yayi Alhaji Baba. Sai ta zauna ai tunda ga waje" Nan kowa ya watse ni nayi ɓarayin da aka bamu, suma duk suka kama gabansu. A zazzaune na shiga na samu su Hajja Mama sunata hirarsu cikin nishaɗi ga ƴan biyu a gefen Batula. Gaskiya ƴan biyu zasu yi kewar Batula sosai itace uwar renon nasu dama. Haka dai muka raba dare muna hira Washegari bayan mun karya kowa yayi wanka, sai su Hajja Mama suka nufi kasuwa bisa jagorancin Anty Sumayya. Ni kuma Hajiya tazo ta kirani na koma ɗakinta dan anata zuwa ganin Amarya. Nice har azahar ina takure gashi Batula da ƴan biyu suka tafi. Matan ƙannen Usman sai ɗan jana da hira suke yi barin ma Maman Usman da take cewa itama mijinta yana india yaje yin wani kos. Tare ma zasu dawo da Usman. Kuma in mijin nata zai koma tare zasu koma ma dinga haɗuwa. Ni dai sai ɗan murmusawa kawai nake yi. Sai wajajen magriba su Hajja Mama suka shigo gidan. "To Iyabo kije ga ƴan uwanki can sun dawo ko?" To Hajiya nagode sosai sai da safenku Maman Usman " Dariya tayi tace. "Muma yanzu duk zamu tafi, sai kuma an kwana biyu zamu leƙo kafin uncle ya dawo." Ina shiga cikin ɗakin da su Hajja Mama suke sai naga jikinsu duk a mace. Gabana a faɗe nace. Hajja Mama lafiya?" "Ina fa lafiya Iyabo. Ke dai ƴannan Allah dai yasa Usman ba da niyyar cutarki ya aureki ba, ko kuma da mummunar manufa ba. Domin magana ta gaskiya mun tsorata sosai." Gabanne ya yanke ya faɗi ras" Kafin ta gama rabe ɗayan biyu Nima nake cewa sai ranar tilitin in Allah ya kaimu Mrs Bukhari ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI Littafi na huɗu (10) MARAƊI Hadiza ta fashe da kukan baƙin ciki a tsakar gidan daidai malam ya gama abinda yake yi a ɗaki ya fito. "Ai baki yi kuka ba wallahi akwai sauran kuka a gabanki. Domin Gwadabe tattarawa zaiyi nan da shekara ɗaya masu zuwa ya koma can Najeriya yanzu haka a ƙauyensu ƴan gundumarsu shi suke son tsayarwa a ɗan takararsu na kansila siyasa Gwadabe ya shiga. Kina nan zaki ga Shafa a Abuja a cikin taron matan gwamnoni ana damawa dasu shashashar kawai. Isuhun da kika raina a baya kika kasa bashi farin ciki ba ga yadda rayuwa ta warware mishi ba, kece baki da rabon arziki. Shi kanshi Gwadabe rabuwarku ce ta ɗaga darajarshi. Duk matar da bata bama mijinta kwanciyar hankali ai ba zata barshi ya nemi arziki ba. Asshi ki dinga nusheta in zata gane" Baba Asshi ta ce. "Malam a dai yi haƙuri wannan karon abun ka ɗauka da zafi. Ni ina ganin ka ba Gwadabe haƙuri ya mayar da matarshi ɗakinta dan Allah. Yarinyarnan fa tana son mijinta" "Babu ruwana ai bani nasata tayi abinda ta ƙure mijinta ba. Dan ɗiyatace bazan bari ta cuta ma Gwadabe ba dan shima ɗanane, yayi haƙuri da'ita ainun" Yana gama faɗar haka ya fice. Baba Asshi ta dubi yadda Hadiza take kuka kamar wata ƙaramar yarinya tace. "Hadiza kuka ba magani bane. Kiyi ƙoƙarin gyara laifinki a wajen Gwadabe tun kafin iddarki ta cika ki samu ya mayar dake. Kar kiyi sake Gwadabe ya kubce miki, mijinkine har yanzu ke kika san logonshi kima share hawayenki kawai" Sai lokacin Hadiza ta ɗanji sanyi a zuchiyarta harma da yamma ta kintsa ta tafi gidan ƙawarta Chima. Da sallama ta shiga ɓarayin ƙawar tata gidan babbane sosai. Ai kuwa ta samu Chima a kwance a kujera ta caɓa adon bazin tana kallo ɗakinta sai ƙamshin turaren wuta yake yi. Sai Hadiza taji tana matuƙar kewar mijinta da ɗakinta har hakan sai da yai sanadin taruwar hawayenta. "Yau uwargidan Gwadabe ce a gidan nawa da yamma haka, ko dai ɓatan kai dai kika yi ne? Dariya Hadiza ta ƙwaƙulo tare da zama. "Wash kya ji dai dashi Chima ni bani abu mai sanyi in sha" Da sauri Chima ta kawo ma ƙawar tata jus harda shayi da ƙaramin kofin tangaran na shan shayin. "Ɗakin kai mai daɗi Chima. Mace bata ganewa sai wata kaddarar ta rabata da ɗakinta ta koma rayuwar gidansu" Dariya Chima tayi tace. "Ƙawata an tuno da zawarci kenan? Hakan yasa na tuno jiya uwar haka kishiyarki ta da matar Isuhu tana gidannan wajen kishiyata. Ta kawo shaddaji daga mali tazo ta kwasa. Ni abinda ya bani mamaki bazin masu geza da shole duk ta ɗiba. Kuma ba bashi ba take ta biya. A bakin abokiyar zaman nawa nake jin labarin ashe har umara suka je dana ɗan doki cikinta" Wata ƙayar kishi ta miƙe tsaye a maƙoshin Hadiza da ƙyar ta haɗiye yawu tace. "Ture maganar Isuhu da ƙazamar matarshi nifa an yanka ta tashi aurenane ya mutu Chima. Yanzu haka Gwadabe yana umara da Shafa' Nan Hadiza ta kwashi labarin komai ta labarta ma ƙawarta kuma bata ɓoye mata kuskuren data aikata ba itama" "Assha kinyi wawa Hadiza. Kin zubar da girma da mutuncin mata, kin watsama iyayen gida ƙasa a ido. Ko duwatsune Shafa da Gwadabe dole ki kaisu bango. Mafitar ɗaya ce kiyi duk iya yinki mijinki ya mayar dake ɗakinki, kibi duk hanyar da zata ɓulle ke inta kama ki tsugunna guiwiyinki a ƙasa ma duk kiyi ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba. Amman kafin su dawo ki zama mace ƴar gaske macen da tasan kanta. Kuma ki koyama kanki danne kishinki a koma inane. Ke baki isa kice sai an faranta miki ɗari bisa ɗari ba. Domin kema ba zaki iya kyautatawa ɗari bisa ɗari ba. Ba zaki ce miji sai dai ya kula dake ke kaɗai ba alhalin itama waccan na da nata hakkin. Kin ganni sau nawa maigidanmu zai kwaso gulmarshi ta maza yazo yana rage murya akan ki siyar mishi da kwana ya kaima kishiya. Ashe in kece sai dai washegari a tsinci gawarki ko? Ni ko bajewa nake yi in samu baccina lafiyayye ke nifa namiji ko kishiya basu isa sunsa hakkinsu ya kaini wuta ba wallahi. Namiji inya kwaso rawar kanshi ki nuna mishi baki sanma yanayi ba. In kika nuna kina damuwa har ya gane logonki kin shiga uku. Dan na fahimci Gwadabe da gayya yake yin wasu abun dan ya kunnaki. Ke kuma sai ki kunnu. Tunda dan hauka har da tsohuwar matarshi kike kishi. Asa ma ɗiyarki sunanta kinƙi ga Shafa tana cin albarkacin sunan ai. Wato na lura yarinyarnan shafa tana da mugun wayo ne, shi yasa tayi miki fintinkau. Tun farko me zaima sa in ba Shafa ta mayar dake jarababbiyar miji ba zata ce ta bar miki kwana harna wata biyu. Ke kuma kika amsa, hakanma bai miki ba harda ɗaga labulen uwar ɗakin kishiya?. Bazan ɓoye miki ba in da nice kishiya ta buɗe mun uwar ɗakina to tabbas saina mareta Allah. Ai uwar ɗakina sirrinane ko haihuwa nayi ni ɗakin yara nake komawa da zama duk wanda yazo barka ina can, ɗakina da mijina yana kulle. Ke kin taɓa shigarmun ɗakina?" Hadiza ta girgiza kanta tace. "A_a ban taɓa shiga ba gaskiya. Iyakacina falo da ragowar ɗakunan" "To wallahi Hadiza ba yabon kaiba uwarɗakina aljannar duniya ce ta more rayuwa duk wani kayan alatun saka nutsuwa da farin ciki a ciki nake sawa, duk sanda mijina ya shiga uwarɗakina sai ya sauke ajjiyar zuchiya kyau da tsarin kawai na iya sashi nutsuwa. Kullum a cikin siyan zanin gado nake domin sake ƙawata ɗakina. Hakan yasa ko jinyar da yayi ya takurama matan akan shi lallai a ɓarayina zaiyi jinya. Dole suna ji suna gani ya tawo nutsuwa yake nema Hadiza. Amman ke har a kan gado kishiyarki take shigowa ta same ku. Ke kuma ki bisu ki gansu suna sumbatar juna." Chima ta ƙwace ta dinga wayar da kan Hadiza. A taƙaice saida ta wanke mata ƙazamin kishinnan nata tas. Kafin Hadiza ta koma gida. Tun daga wannan rana sai Hadiza ta tattare kayanta da yara ta yi komawarta ɗakinta. Malam na dawowa Baba Asshi take sanar mishi ga fa halin da ake ciki. "A kyaleta. Dama can ya dace ace tayi iddarta. In Gwadabe yaji tausayinta ya mayar da'ita ɗakinta shikenan. In kuma yaji bazai sake rayuwar aure da'ita ba ba zan yi mishi tilas ba sam dan na fi son tayi aure a waje can bare ya gasata" Haka Hadiza ta shiga gyaran ɗaki da gyaran jikinta da taimakon Anty Badi'a. Har kayan ɗaki da fasalin ɗaki saida Hadiza ta canja. Sannan Anty Badi'a taci gaba da bata shawarwarin daya dace. Ta kuma sake ziyartar Chima ta sake ɗorata a layi mai bullewa. Ranar talata da yamma lis Hadiza na kofar kitchen ɗinta tana soya miyar kaji sai ga sallamar su Shafa da Gwadabe da kayan tsarabarsu niƙi_niƙi. Hadiza ta kalli Gwadabe da kyau. Shi kuwa yana kan amsa sannu da zuwan matan gidanne. Dashi da Shafa duk sun maƙala haƙoran makka. "Shafa kune a tafe? Maraba lalenku da zuwa. Ina Iyabo ban ganta a bayanki ba?* Cewar Hadiza data isa inda suke tsaye da fara'arta harda amshe ma Shafa jakar kaya. Ba Shafa da Gwadabe ba hatta matan gidan sun yi mamakin wannan lamari. Cikin dariyar yaƙe Shafa tace. "Tana najeriya ba da'ita muka tafi ba ai. Ya yaran kuma ina su Toye da ummi?" "Suna can cikin gida wajen Baba Suwaiba. Gwadabe sannunku da dawowa ku shiga bari in kawo muku abinci" Shi dai goga bai kulataba Shafa ta buɗe ɗaki suka shiga. Bata ma zauna ba dai ta ɗan soma kakkaɓewa Gwadabe kujera dan ya zauna. Yana zama yaran suka shigo da gudu suna murnar ganin iyayen nasu. Hadiza ce ta biyosu da katon tire cike da kayan abinci ta dure a gabansu. Sai ta ɗauki plate zata zuba musu Gwadabe yace. "A_a ki bari Shafa zata zuba mun nagode ƙanwata. Baby zuba mun abincin yinwa nake ji" Yawu Hadiza ta haɗiye tare da yin murmushi. Shafa ta zuba mishi farar shinkafa da miya lafiyayye. Ta dure mishi a gabanshi, ta nufi hanyar fita. "Ina kuma zaki kinsan abinci zanci?" Shafa ta dubi Hadiza ta dawo da kallonta ga Gwadabe "Wanka nake son in yi kasan na gaji da yawa Baby" Dariya Gwadabe yayi yace. "To jeki amman kar ki daɗe in na gama cin abincin zanje inga malam" Shafa ta tafi wanka Gwadabe ya mayar da kai wajen cin abinci shi. Bai gama ci ba ma Zulƙi ya kira wayarshi nan ya fice ya bar Hadiza a zaune kamar gunki. Murmushi tayi a ranta taji zafi amman tasan abinda Shafa da Gwadabe su ka yi mata daidai ne ita ta ja ma kanta zubewar mutunci. Ɗakinta ta koma taci kuka kamar ranta zai fita da ƙyar ta rarrashi zuchiyarta ta tuttura abinci tasha ruwa ta kwanta Gwadabe kuwa bayan ya gama amsa wayar Zulƙi sai ya shiga makarantar Malam. "Gwadabe mutanen makka kun dawo? Kai masha Allah sannunku da dawowa" "Yauwa Malam da fatan na sameku lafiya, ya dalibai?". Da dariya Malam yace. "Gasunan wasu ma aka sake kawowa ka gansu nan. Sai ka dawo ka tarar da Hadiza ta koma ɗakinta ko? To bani bane nace ta koma ba. Dama shari'a ta bata damar zaman idda a gidanka. Bayan tafiyarka ta shiga damuwa mai tarin yawa. Ƴan uwan duka sun juya mata baya. Ni daɗina da Allah yasa Fhatsima bata raye wannan abun ya afku da yanzu ta sata a damuwa. Sai kayi haƙuri kaci gaba da ciyar da'ita zuwa lokacin da iddarka zata sauka a kanta." "Babu damuwa malam. Ni gobe ma zan tafi Takai akwai meeting da za'ayi da mai girma Gwamnan Kano kuma akwai buƙatar zuwan ƴan takara. Gobe asussuba zan kama hanya sai a taya mu da adda'a " "To to to Allah ya tsare yasa ayi taro lafiya a watse lafiya. Ni ko kasan halin da Iyatu ta jefa gyatumarku kuwa? Fitsararriyar yarku Halima ta kirani tana kuka wiwi ta labartamun halin da ake ciki." Gwadabe yace. "Na sani Malam" Nan ya labarta mishi shi labari.A hakan harda tsarabarta a cikin tsarabar da yayo zai sa Bara'u ya kai mata ba tare da ance shine yayi ba" "Hakan da kayi yayi daidai tabbas ka haifu Babala abinda ta shuka ne take girba. Kar ka kuskura ka nuna kanka ban amince maka kaje cikin gidannan ba. Kaci gaba da yi mata alherin ɓoyen ladanka na wajen Allah, amman kar ka kuskura kaje inda take. Tashi kaje" Sum_sum Gwadabe ya fice. Yana fitowa yaci karo dasu Mammada nan fa suka ɓalle da hirar yaushe gamo. Sai da akayi sallar magriba suka samu damar shiga gida. A daren Gwadabe ya raba tsaraba tsab ya umarci Shafa da ta shirya musu jaka zasu tafi Takai akwai meeting da za'a gabatar. Ai kuwa hakan akayi bayan ta dawo daga kaima Hadiza jakar tsarabarsu ita da yaranta sai ta shiga haɗa musu kaya da tsarabar ƴan takai ɗin ma. Washegari sassafe suka kama hanyar Takai. Sai da Hadiza ta fito tsakar gida da safe take jin labarin tafiyar tasu a bakin matan gidan. Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba a wannan ranar Hadiza tayi kukan nadama yafi cikin duro. BABALA:. Tana zaune a ƙaton katafaren gidan Yaya Hambali ita da Da'u da Yaya Halima mai gadi ya hanasu shiga. Ga duhu ya soma rufawa Yace masu gidan basa nan sun fita shine suke zaune suna jiransu. Sunfi awa ɗaya a zaune sai ga motar Hambali ta karaso. Layla na gaban mota Goggo Iyatu na baya ita da Tanimu wan Laylan. Mota Hambali ya buɗe yana yaƙe baki ya nufi su Babala. "Wai ina zaka je haka ne Hambali ba da kai nake yi bane wai?" Da tsawa Layla take magana bayan ta buɗe murfin motar ta fito. Hambali ganin ran Layla ya ɓaci sai yayi saurin komawa baya. "Uhm su Babala ne baki gane su bane?" Ya faɗa yana wata doluwar dariya. Idanunshi yaji kwalli harya zazzago. "Sabida Babala ce zaka wani fita ka barni a cikin mota, basu da ƙafane ko basusan hanyar cikin gidan bane? Dallah wuce ka koma ka shigar damu ciki" A guje yana saɓa malum_malum ɗinshi ya shige mota suka ja megadi ya buɗe musu suka shige. "Amman dai Allah ya tsinema Layla da Iyatu yaron nawa ne suka mayar dashi haka? Shikenan ya zama dole ku taso mu koma gida zai fi mana na haƙura da shiga" "A_a Babala mu dai shiga mu miƙa ƙoƙom bararmu ko Allah zaisa a dace takaicin yayi yawa" Cewar Yaya Halima kenan. Da ƙyar suka ɗaga Babala tsaye jikinta yayi nauyi ga ba guiwa. A falo suka samu Goggo Iyatu da Layla da Tanimu suna kan kujera suna shan ac ga jus duk suna kurɓa. Shiko Hambali yana gefen ƙafar Layla kamar me roƙon gafara" ƙwafa Babala tayi ta zauna. "Shin menene hakan Hambali kake zaune a gabanta ta gurfanar dakai kamar mai roƙon gafara. Iyatu amman dai Allah ya tsine miki albarka kwashasshiya kin cutar dani kin zalunceni, na saku a inuwa kun turani rana Ashe Gwadabe yayi gaskiya da yaƙi yarda fur ya auri wannan ƴar taki mai halin ɓera. Yau ni kika raba da ɗana kika tarwatsamun kan ahali kika tagayyaramun ƴaƴa?" Kukane yaci ƙarfin Babala sai Yaya Halima ke rarrashinta Da'u kuwa yana dai kallon komai. "Baki soma kuka ba Yaya wallahi. Hambali ya rabu dake har abada dan bokan da yayi aikin ma ya ɓar ƙasar kuma aikinshi babu bokan da ya isa ya warware shi. Ai nasan kinsan hakan tunda ana ganoki a tudu da gangare na bokaye kina godonsu akan a karya wannan asiri. Hmmm ke kin manta duk abinda kika yi ne ko sai na tona miki asirinki a gaban ƴaƴan naki ne?" Babala tayi saurin ɗagowa ta dubi Goggo Iyatu tace. "Duk mai ya kawo wannan maganar Iyatu. Shin duk da abinda na aikata ya dace ki rabani da ɗana kenan?" Shewa tayi tace. "E ya dace mana sosai ma kuwa. Yau kika saba rabuwa da ɗanki ne Yaya? Ba ga can Gwadabe a Maraɗi yana rayuwarshi ba. Kinyi mai duk abinda zaki yi mishi, kin cutar dashi ta fanni da ban daban, kin mai asirin rariyar hannu dan masifa. Da yake ke mai kwaɗayice shi yasa kika damu da shi wannan ɗin. Asiri ai gaskiya ne, kema kinsan gaskiya ne tunda babu abinda baki birne ba. Haka shima Hambalin babu abinda bai birne ba dan neman shahara. To lefine mu dan munyi mishi?" Layla tace. "Baba ki dena ɓata yawun bakin ki akan waɗannan mutanen?" Yaya Halima ta taso tace. "Babalan ce wannan mutanen dan ubanki?" Ai kafin ta rufe baki Yaya Hambali dake ta zazzare idanu yana kallonsu sai yayi firit ya miƙe ya ko kwaɗama Halima mari ya sake. Babala data zuchiya sai kawai ta rufe Hambali da dukan takaici da baƙin ciki. Ita ce ke dukanshi amman kamar ita ake duka tsabar yadda ta yi laushi. Kallo daya za ka yi ma Babala ka fahimci tana cikin damuwa." Layla da Iyatu ne suka jaye Hambali. Layla ta umarceshi da ya shige ɗaki. Zungui_xungui ya shige ciki. "Ku fice mun daga gida. Sabida tsabar rashin kunya kuzo har gida ku dakarmun mijina haka akeyi. Sai lokacin Da'u ya buɗe baki zaiyi magana Babala tace. "Rabu dasu gasu ga Hambalin. Kamar yadda duniya taimun atishawa, komai daren daɗewa suma zata yi musu. Halima muje mu dangana babu komai" Suka sa kai suka fice Babala sai kuka kawai take yi. Ga dare ya rufa sosai ga zafin zuchiya Shigarsu Takai kenan suka gamu da Gwadabe shima saukarshi kenan a achaɓa, ya kai Shafa gidansu. Da idanu ya bisu suma suka bishi da nasu idanun barenma Babala wacce har kusan tuntuɓe tayi. Yadda ya gansu a lalace a rame abun ya dakeshi sosai. Yana ji kamar yaje karesu, duk da yaga salama a idanun Babala kasa takawa yayi, ko yayi musu magana. Ta ɓangarensu kunya da mamakin sauyawar Gwadabe ce ta hanasu yi mishi magana. Sai dai fa suna tafe suna waigenshi, yana tsaye har saida suka shiga gida. Wasu zafafan hawaye suka gangaro a kumatunshi masu zafi. Ta bayanshi yaji an dafa kafaɗarshi." Mrs Bukhari ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU (11) IYABO:. Babu guiwa na ƙarasa gaban Hajja Mama nace. Ku yi mun bayani yadda zan fahimta wani abun kuka gano ne Hajja Mama? Gara in sani tun kuna nan in auren ba mai yiwuwa bane in biku tun wuri" Hajja Mama tace. "Iyabo ke wai kinga kyau da girman gidan da matan Usman suke ciki kuwa? Ga motocinsu a tsakar gidan. Ke ko wacce da ɓarayinta. Ba wannan ba Matarshi ma fa kamar balarabiya ce dan gaskiya ba da fulani tayi kama ba, dan larabci ma take yi ma wani farin yaro. Baki ganta ba siririya kyakkyawa. Ɗakinta danƙare da kayan ƙawa. Wallahi ni sai na rainaki da kayan ɗakinki a cikin wannan gidan. Kinji dalilin tsoratarmu gaskiya " Idanu na lumshe na sauke ajjiyar zuchiya mai nauyin gaske. Harga Allah ni tunanina wani waje daban ya dosa. Duk da dai labarin da suka bani yasa guiwata tayi sanyi take saina raina kaina da kaina. Ammam dana tuno da balarabiyar matar tashi nima ya ganni ya auroni, kuma da balarabiyar matar tashi yake shagaltuwa wajen kallona harma ya sanar dani nice ainihin zaɓinshi tun na ƙuruciya. Sai na sake sauke ajjiyar zuchiya. Hajjja Mama ta dafani tace. "Amman ba wai ina nufin ki raina kanki bane ko mu mun rainaki ba a_a. Mun sanar dake ne dan ki sani ki san yaya ma zaki tunkareta duk da sauƙin ta ba tare zakuita zama ba. Duk da ganin tamfatsetsen gidannan yasa na soma tunanin zaiyi wuya Dr ya barki a India din_din_din alhalin ga sauran matan a gida Najeriya. Ina ganin hakan kuma kamar zai iya haifar miki da baƙin jini sosai a wajen matanshi. Ke dai ki iya takunki a sannu, kar yaje ya jawo miki baƙin jini a cikin dangi. Ajjiyar zuchiya na sake saukewa a karo na barkatai dan ba ƙaramin tsinkar mun da zuchiya suka yi ba. Hajja Mama ta daɗe tana yi mun hudubobi nasu na ƴan duniya, da dabarbarun zama da miji, da su kansu kishiyoyin, da kawar da kai akan duk abinda bai shafeni ba, wanda ya shafenin ma ta horeni da yin haƙuri. "Amman fa bance ki mayar da kanki banza bane. In miji yayi miki yau kika ɗaga mishi ƙafa, gobe in yayi miki ki zaunar dashi ya fahimceki ki fahimceshi gaskiya. Haka suma kishiyoyin bana nufin kita shanye takaici yazo ya haifar miki da hawan jini a banza. Sannan ki gina kanki, dan gwal ɗinnan, dan filinnan kiyi ƙoƙari ki mallaka sabida halin rayuwa, miji zai iya sakinka, ko ya mutu, ko ya juya maka baya ma. In kana da naka na kanka abun yana zuwa da sauƙi. In akwai sana'ar da kike ganin ya dace acan ɗin in kuka nutsa sai ki gabatar mishi da sana'ar ki dinga turo kaya ana siyar miki ana tura miki kuɗinki, ko kuma ki dinga siyen kadarorinki kina gina rayuwarki. Ta daɗe tana bani baki. Washegari sassafe suka wuce sai ni da ƴan biyu ƙwalam, ra baƙunta na damuna, duk da ni daɗi naji ma da Alhaji Baba yace in yi zamana a nan. Tun kafin in ga matan Usman tsoronsu ya ɗarsu sosai a raina. Da dai na gaji da zaman bayan mun gama waya da Usman saina fita falon na tadda ƴar aiki tana ta goge_goge Hajiya kuma tana sama. Sai kawai na shiga kitchen na soma taya Luba abinci. Ni nayi ma Alhaji faten acca da jan wake, yaji Aleyiwo da hanta. Na dama mishi kunun acca na zuba a flaks kasancewar yana ɗauke da ciwon siga ire_iren cimsrshi kenan. Ina kan haɗa plate Hajiya ta sakko. "Luba Alhaji zai fita kin gama ne?" Ganina a kitchen ɗin yasa ta faɗaɗa fara'arta. "A_a Iyabo kece a kitchen? Ai da kin bar Luba tayi aikinta kin huta. Yanzu da Usman zai zo ya taddaki a kitchen da inya dinga mita a gidannan har sai mun gaji" Luba tayi carab tace. "Nayi _nayi ta bari ƙi tayi Hajiya" Hajiya ai ba komai. Dake ban saba zaman ba sai duk na gaji shine nace bari in kama mata aikin " Murmushi tayi tace. "Ikon Allah Luba kinga mun samu suruka mara son jiki. Matan yaran gidannan ko wani ɗan taro aka haɗa sai dai a siyo abinci a hotel. Ai ko Usman ne zai shigo ƙasar a hotel ake sissiyo abinci dan ganda." Ni dai kaina na ƙasa ta gama shi mun albarka ta koma falo. Dani da Luba muka jera komai a babban daining ɗin gidan Alhaji Baba sai shi mun albarka yake yi tare da yabon abinda nayi. Tun daga ranar na karɓe girkin Alhaji Baba a hannun Luba ni ke mai girkinshi. Yana ci yana jin daɗi sosai. Kwanana Bakwai muka wayi gari yau su Usman zasu shigo ƙasar. Tun suna Airport muke waya dashi har zuwa shigansu jirgi kafin yayi mun sallama. Ina zaune kunyar in fita ince zan yi mishi girki nake ta yi. Sai ga Luba ta shigo da sallamarta. "Anty Iyabo Hajiya tace in sanar dake sun tafi ƙauye ita da Alhaji Baba. Mahaifiyar mai wanki da gugan gidannan ce Allah yayi mata rasuwa, wai sai gobe zasu taso daga nan zasu biya wani wajen." Ai sai naji daɗi sosai. Ayya Allah ya jiƙanta nima yanzu nake son in fito ki taya ni girkin tarbar Usman ai" Dariya Luba tayi tace. "Tabb su Uncle yau har kitchen za'a shiga ayi mishi girkin tarba? Tabb shi da wata rana sai ya shigo ƙasar zai kwashi matan ya kaisu gidan cin abinci ma" Mamaki sai ya kamani. Muna kitchen ina ferar dankalin turawa, Luba na zuba ma kaza nono da kayan ƙamshi tana bani labarin abubbuwa daya kamata ace na sani, da kuma yin taka tsantsan sosai. Ni dai mamaki duk ya bi ya isheni. Faten dankalin turawa da niƙaƙƙen naman saniya nayi. Sai nayi shinkafa kaza . Nayi mishi zoɓo mai kyau yaji abarba da inabi bushasshe. Sai bayan la'asar muka kammala aikinnan na shiga wanka na bar Biyu tare da Luba a falo suna turara falon da turaren wuta. Sai da nayi sallar la,asar kafin na soma shafe_shafen mai da turarukan ƙamshi, da humrori harda humrar matan aure. Sai da na gama mulke jikina da Humrar matan aurennan na tuno sister Badiat Ibrahim tayi gargaɗi akan sai in zaka turakane zaka shafa ba'aso kowa yaji ƙamshin face mijinki, ko kishiyarki ba'aso ki shafa ranar kwananta gudun kar a shiga hakkinta. Dan wannan humra wani key ne na buɗe sha,awar ɗa namiji, hanyace ta sawa miji ya zamema matarshi ɗaye manna, tana da tasiri ainun. ( Babu boka babu malam wallahi Allah ɗaya ne babu wani abu na surkulle a ciki. Sanin aikine da sanin itatuwa masu tasiri ga ma'aurata. An sanmu Kanuri muna gaba_gaba wajen mallakar zuchiya da ruhin ɗa namiji ta hanyar ƙamshinmu na jikinmu, da ƙamshin gidanmu. Me so tayi magana ina ɗiba a ƙaramar kwalba dan kowa ta mallaki nata) ina cikin rabe ɗayan biyu kawai na jiyo muryar Usman yana wasa da biyu. Gabanane ya yanke ya faɗi duk saina dibibice. Sake kayan zanyi ko in fita a haka kawai? Luba ce naji tana kirana da ƙarfi babu shiri na fito ko mayafi babu. Da matarshi muka soma haɗa idanu tana tsaye shi kuma yana zaune ƴan biyu na cinyarshi sunata zillo. Kallon sama da ƙasa tayi mun irin kallon tsantsar wulaƙancinnan dan a zahiri kyakkyawace baƙa mai dogon hanci da dara daran idanu. Idanuna na mayar kan mijinmu shima ni yake kallo amman kallon burgewa. A hankali na tattako da fara,ata na wuceta ina karkaɗa abun duniyar da ni shi kaɗaine kyauna wanda nayi imanin ya girgizata ga ƙamshin humrata daya sumar da'ita. Saida naje daf dashi saina juya mishi bayan nawa ita na fuskanceta da dariyata. "Antyna bari in soma dake barkanku da dawowa da fatan kun dawo lafiya?" Na ƙarashe ina dariya. A zuchiyata kuma duk fa na raina kaina dan harna soma kokonto akan Usman. "Lafiya lau Amarya ya baƙunta?" Ta faɗa da salon cinye kishi. Kallon Usman tayi tace. "Gaskiya ka iya zaɓe wannan karon lutiya kaji sha'awa kenan. Naga tana da ƙiba masha Allah" Ni nasan magana ta caka mun. Shi ko gogan naka sai ya saki murmushi yana wani jin daɗi. "Sannu da dawowa ango mijin Amarya ya hanya?" Ai kafin yayi magana sai ta kwashe da uban dariya harda rufe idanu. Shi kuma yayi lub a kujera sai shaƙar ƙamshina yake yi idanunshi har sun sauya kala. "Lafiya Honey meya faru?" Ya tambayeta murya ƙasa_ƙasa "A_a ba daku bane a waya ne aka turo wani abun dariya shine ya bani nishaɗi. Ni kam ina buƙatar watsa ruwa" Murmusawa nayi na bita da idanu, itama ni take kallo. Zama nayi abuna ina jiran abinda zaice. "To ko in kai ki gidane ni sai in dawo? Tun a Airport nace in kai ki gida kin ƙi. Gimbiya kaita masaukin ki ta watsa ruwa. Ina Luba taje mota ta dakko miki akwatinki" Ni dai ina zaune ina kallonsu kar. "A_a ta barshi kawai. Sai ka tawo dama na zaci Alhaji Baba na gidanne mu gaisa" Tana gama faɗin haka ta yi ficewarta. "Asma'u!! Asma'u!! " Ko juyowa batai ba. Kallona na dawo dashi gareshi, ni yake kallo harda ƙanƙance idanunshi. Yayi wani kyau na musamman. "Ya akayi Gimbiya. Duk kin kashe mun jikina da ƙamshinki sai wani kasala ke sakkomun. Kinyi kyau fiye da da. Da wanne turare kike amfani haka mai sanyin ƙamshi haka? Murmushi nayi nima na juya da kyau ina kallonshi nace. Da yaushe kenan yallaɓai?" "Da kafin in aureki mana" Dariya muka yi tare. Ya kama hannuna da hannunshi masu ɗumi ya riƙe. Lumshe idanuna nayi. Kun dai san mutuniyar taku ba daga nan ba, balle an jima ba'a haɗu da rijalu ba.( Ummu nabeeha ni Iyabo dake nake) Da ƙyar na buɗe idanuna na kalleshi. Shima ya shige cikin kujera yana ta aikin kallona ga ƴan biyu sai gwarancensu suke yi mana. Yanzu dai muje kayi wanka sai kaxo kaci abinci nayi maka girki mai daɗi" Kamar rakumi da akala haka ya zamemun. Ko wankan da ƙyar na rarrasheshi ya shiga kun gane ai? Hahaha Kafin ya fito na fita tsakar gidan ina tambayar da wacce motar suka zo. Mai gadi ne yake sanarmun a motar Hajiya Asma'u ta tafi gida. Ina komawa ciki na sameshi a kwance a gado daga shi sai tawul a jikinshi. "Ina jakar kayan nawa ko ba ita kika je ɗakkowa ba.? A hankali yake magana kamar bacci yake ji, ko kuma wanda ake yima susa a takashi. ko kuma ya kwaso gajiya ne ƙila daga wajen aiki, tunda jiya ma a asibiti ya kwana. Hajiya Asma'u ta tafi da motar da kayan ke ciki. Ƙila ta manta ne. Kazo muje kaci abincin ko?" "Ta tafi mun da kaya fa?". Ya faɗa da mamaki. Ni kawar da zancan nayi ta hanyar taimaka mishi yasa kayanshi, bayan na bashi kulaccam ɗina ta musamman ya shafe jikinshi dashi, yanata santin ƙamshin. Muka wuce daining na zuba mishi abincinshi nima na zuba nawa. "Ya baƙunta dai. Da fatan Family na sun karɓeki hannu bibbiyu ko?" Sai da na haɗiye abincin bakina kana nace. Sun karɓeni fiye da tunani na ma. Gaskiya akwaisu da karamci" Murmushi yayi yana kallona. "Kinga Asma'u yau ko? Ita Suhaila ai kun haɗu a sha'anin biki ko?" A_a za dai mu haɗu gobe in sha Allah?" Cokali ya ajjiye yana tauna abinci yana kallona so yake ya gama tauna abincin nasan ya jefo mun tambaya. Ai kuwa ilay "Bata zo buɗar kai bane ko Yaya. Kina nufin bata zo gidannan ba.?" Gaskiya ko tazo bamu haɗu ba. Babu mamaki abubbuwane sukai mata yawa" Dariya kawai yayi tare da kurɓan zoɓo ya girgiza kai kawai. "Wacce ƙasa kika taɓa fita shine ko labari baki bani ba har sai da kuka je ofishin yin paspo tukunna. Ko umara kika je ne uhm?" Ya tambaya yana dariyar zolaya. Cikinane ya karta mun, sai da na ɗan riƙeshi kaɗan kafin nace. Umara na taɓa yi. Na mance ne ban sanar maka ba." "Okay to naji kince gobe Suhaila zata ganki. Ba yau kike son tarewa da angon naki bane, ko baki shirya bane?" Ya kafeni da idanu take na ƙware. Saida na daɗe ina tari kafin ya faɗa mun. "Sannu kiyi a hankali" Sai da na dawo cikin hayyacina kana nace. "Sai su Alhaji Baba sun dawo gobe tukunna zamu tafi" Dariya yayi harda tafi. "Au so kike yau in kwana a gidannan kenan ko mu yi abun kunya?" Da dariyata nace. "Akan me ga matarka can tana jiranka." Hararar soyayya yayi mun. A haka dai mu ka ci abincinmu muna hira har akai sallar magriba. "To zanje masallaci daga can zan wuce can gida in dubo Antynki da yara. Zan dawo mu kwana anan ɗin tunda dai haka kike so muyi abun kunya" Kafin ma in yi magana ya fice. Da sauri na shiga ɗaki na tura mishi text akan ya zauna tare dasu, nima zanyi zamana anan har zuwa ranar da zamu juya tunda yace kwana uku zaiyi ni na barma Hajiya Suhailat kwanan. Ina turawa na datse wayata na ta da kabbarar Sallah. Bin Usman:. Yana idar da sallah ya ɗauki motar Hajiya ya nufi gidanshi dake Abuja kwatas. Gidan sama ne babban gaske. Motarshi na shiga harabar gidan yaranshi suka fito a guje zuwa tarbarshi. Da dariya ya tarbesu yana shafa kawunansu tare da tambayar lafiyarsu. Gaba yayi suna biye dashi a baya har zuwa falon ƙasa wanda anan matattakalar hawa benen take. A gefe_da gefe ko wacce mace matattakalar hawa samanta da ban. Shi mai gidan ɓarayinshi na cikin babban falon gidan. A gefen nashi ƙofar shiga ɓarayin iyabo yake wanda kafin zuwanta ƴan uwan Hajiya Suhailat ne maza a ciki suna karatu a garin. Yanzu sun koma bq da zama wannan ma ya sake dafa Hajiya Suhailat sosai. A babban falon ya tarar da Mus'ab ƙaninshi yana zaune yana kallon labarai dama mayen labaraine. "Sannu da shigowa Yaya Usman. Na ganka kai kaɗai ina Amaryar tamu mu da muke ta dakon zuwanta?" Zama Usman yayi kusa da ɗan uwanshi yara kuma suka wuce sama wajen iyayensu. "Ka sassauta muryarka kar Suhailat ta hanaka kallo a falonnan ni dai na faɗa maka" Dariya Mus'ab yayi yace. "Ta kuwa ɗauka da zafi itama fa bayan an kawo Amarya. Kasan matar Usman karami shegen surutu ne da'ita tazo gidannan tana ta labarin amaryar. A taƙaice ma ƙannenta sun tattare kayansu sun bar gidan. Ƙanwarta Naja dai tazo tun ranar bikin. Mu kammu fishi take yi damu fa. Anty Ma'u ma ko gaisuwata data shigo muka haɗu a wajen ajjiye mota bata amsa ba sai tsaki da harara dama kasanta bata da daɗi." Shiru Usman yayi yana nazari ranshi ya ɓaci matuƙar ɓaci. Menene laifi dan yaga mace ya aureta kamar yadda suma ya auresu? Ya ga dukkansu sun ɗauki auren da zafin da bai yi zato ba ma. Ita kanta Asma'un ya daddanne abubbuwan da tayi mishi a india da dama. Gashi cikinsu babu wacce ta sakko da zummar tarbarshi ma. Kunji irin gidan da Iyabo ta sake faɗowa Ko yaya zaman zai kasance oho" MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU (12) GWADABE:. Da sauri ya juyo sai yaga ashe Bara'u ne a bayanshi. Bai ga Bara'u a cikin daɗi ba, kamar yadda shima ba'a cikin daɗin yake ba. Juna suka zuba ma idanu cikinsu ko wanne na son jin damuwar ɗan uwanshi. ", Gwadabe ya dai na ganka tsaye kana sharar hawaye? Ai godema Allah ya kamata kayi. Kai da ganin su Babala kasan sunyi nadamar abubbuwa da yawa. Komai fa ya lalace kai Layla har zane Yaya Hambali take yi. Dukiyar ma daya tara ta kusan ƙarewa tas in faɗa maka." Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke. Tare da kallon Bara'u da kyau yace. "Wani al'amari marar daɗi na shirin tunkaroni, da ganin fuskarka kaji labari mummuna Bara'u meke faruwa?" Murmushi Bara'u yayi kawai ya ja hannun Gwadabe har zuwa ƙofar gidanshi, suka zauna a kututture tare da fuskantar juna. "Na zaunar da kaine dan gudun kar in yi maka bayani daga tsaye a samu matsala babba. Amman mu musulmaine dole mu yadda da ƙaddara duk muninta da kaifinta. Asalima rayuwar gabaki ɗayanta jarabawane ranar lahira kuma ranar karɓar sakamakone. Gwadabe Iyabo ashe ɓata tayi an nemeta sama ko ƙasa an rasa. Wallahi Gwadabe da ƙyar na kawo kaina Takai da naji mummunan labarinnan" Gwadabe bai gama jiba numfashinshi ya ɗauke Bara'u sai ganin Gwadabe yayi lu ya faɗi ƙasa wanwar. A guje ya shiga cikin gida, Sakina na bakin bambu tana ɗiban ruwa. Bara'u ya warce moɗar cike da ruwa ya danna da gudu. Sakina ta biyoshi a guje dan ganin meke faruwa. Gwadabe ta gani shanshar a ƙasa Bara'u na shafa mishi ruwa a maɗigarshi. Da sauri ta fito babu ko mayafi. "Subhanallaah meke faruwa Bara'u " Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke ya buɗe idanunshi yana kallon Bara'u da Sakina da suka tusashi a gaba. Hawaye ke bin kumatunshi ƙaƙas kamar ƙaramin yaro mai shan mamma in yi muku hausar ƴan Ghana. "Alhamdulillah. Taso mu shiga daga ciki kaga mutane har sun soma ɗan taruwa kasan ƙauye da gulma." Gwadabe dai babu kalma zungui_zungui yabi Bara'u da Sakina zuwa cikin gidan. A jikin garu ya jingina. "Bara'u kace fa Iyabo ta ɓata sai kace wani ƙwallo ɗan mutum ace ya ɓata. Yaushe kuma a ina kaji?" A mugun ruɗe Gwadabe yake magana yana jijjiga Bara'u. Sakina kuma ta saki salati da tattafa hannaye tare da riƙe haɓa. "Bangane Iyabo ta ɓata ba. Bara'u kayi mana bayani" Kai Gwadabe ya dafe tare da ɗaga kai sama hawaye sai sharara suke yi ta gefe da gefen fuskarshi. "Ya Allah. Bara'u zuchiyata fashewa zata yi. Bara'u ka kaini asibiti zan mutu" Tashin hankali gaga _gaga Bara'u da Sakina suka yi asibitin Takai da Gwadabe. Abu kamar wasa ba sai ƙaramar magana ta ke son zama babba ba. Kafin wayewar gari Gwadabe ya fice a hayyacinshi sosai. A kusan tsaye Bara'u ya kwana a kanshi. Sai da safe gidansu Shafa suka samu labarin halin da Gwadabe yake ciki. Afujajan Shafa ta ƙaraso asibitin ta zo ta samu Gwadabe ya samu bacci Bara'u na zaune a gefen gadon ya zuba tagumi. "Yaya Bara'u wai me ke damunsh ne haka naga lafiyar Allah muka rabu dashi ya saukeni a gida?" Ajjiyar zuchiya Bara'u yayi ya dubi Shafa yace. "Wallahi Shafa iyabo ce ta ɓata aka nemeta aka rasa ta ma jima da ɓatan. Yau na shiga Kano kwatsam na haɗu da ƙaninta shine yake sanar mini halin da ake ciki, anata cigiyarta a gidan rediyo" Salati Shafa tayi tayi shiru tace. "Allah sarki duk inda take Allah yasa tana hannu mai kyau. Oh baiwar Allah kenan ko menene silar ɓatan sai Allah" "Ana dai zargin wai kishiyarta ce tayi mata kurciya ta bazama abun damuwar da goyo a bayanta ga mijin nasu baya nan bai san ma me ake ciki ba' Ashe Gwadabe ya farka sai ji suka yi yace. "Allah zai saka mata koma wanene yayi silar ɓatanta. Na kaɗune ainun da wannan labarin na bagatatan." Bara'u yayi saurin duban Gwadabe yace. "Gwadabe kayi haƙuri mu bar maganar zuwa ka samu lafiya. Likita yace mun kar ayi wata maganar da zata ɓata maka rai kayi haƙuri kayi shiru ga Shafa. Ni bara in kira likita yazo" Yana gama faɗar haka ya miƙe ya fita. Shafa ta dawo bakin gadon ta zauna suna fuskantar juna. "Haba Baban Abba in banda abinka ai adda'a ya kamata ka dage mata dashi domin babu abinda yafi ƙarfin Allah. Ita kuma adda'a bata faɗuwa ƙasa banza. Hakika na tausayama Anti Iyabo sosai, na kuma tausaya ma danginta dan ɓatan rai uku bafa wasa bane. Abinda zamu yi shine tunda Yaya Bara'u yasan ƙauyen da take sai mu ɗunguma muje ayi musu jaje ko babu komai ai ta haifa maka yara har uku, kuma sune kan gidan tunda sune manya" Shafa ta dinga kwantar ma da Gwadabe hankalinshi har sai da Bara'u da Likita suka shigo tayi shiru. "Yanzu meke maka ciwo Gwadabe yaya kake jin jikin naka?" Likita ya jefo mishi tambayar. "Ina jin jiri sosai daga kwancen da nake, sai matsanancin ciwon kai, ga faɗuwar gaba" "Assha sannu Allah ya sauwaƙe. Dan Allah duk abinda ke zuchiyarka ka daure ka cire ko dan ƙoshin lafiyarka jininka ne ya hau sosai a taƙaice ka kamu da ciwon hawan jini na farat ɗaya a sakamakon jin mummunan labari. Zamu ɗan riƙe ka mu kula da kai tukunna sannan zamu ɗauraka bisa magunguna. Ku kuma da kuke tare dashi ku kula wajen tausarshi da rarrashin shi." Likitan dai ya ɗanyi gwaje_gwajenshi yace a samu abinci a ba Gwadabe yaci zai sha magani. Ai kuwa likitan na fita Sakina ta shigo kici_kici da kayan abinci. Shafa ce ta zuba mishi kokko da lafiyayyen ƙosai. Bara'u ya taimaka mishi ya jingina da gadon. Nan aka shiga tata ɓurza dashi, shi yana ya ƙoshi, su suna ya daure ko babu yawa yaci. Ƙosai biyu da kokko rabin kofi yasha da ƙyar, sai maganinshi da yasha, bai jima ba bacci ya sureshi. "Wallahi jiya ban rintsa ba. Bara'u ai ya kamata mu je mu can ƙauyen da abin ya faru ko?" Cewar Sakina kenan. Shafa tace. "Nima nace mishi muje ayi musu jaje sannan a jiyo ko akwai wani labari. Yanzu dai da zaran ya samu lafiya ai sai mu rankaya mu je tunda kai kasan garin. Kamar dai wasa sai da Gwadabe ya kwana uku a asibiti kafin aka bashi sallama Meeting ɗin da bai samu halarta ba kenan. A ranar da za'a sallameshi Chairman da kansila Zulƙi suka zo dubiya asibitin Shigowarsu kenan Da'u da Yaya Halima ma sun shigo duba Gwadaben kuma Babala ce taji labarin a gari shine ta wakiltasu suje su duboshi. Mamakine ya kashe su ganin yadda Chairman da kanshi shi ya biya kuɗin sallama. Sun dai san Zulƙi abokin ƙuruciyar Gwadabe ne, amman basusan meye alaƙar Gwadabe da Chairman ɗin ba. Basu samu ganawa da Gwadaben ba dan basu samu kallon arziki ba ya dai amsa musu gaisuwarsu baya ga haka baice komai ba. Da shirun yayi yawa ne sai Halima tace. "Da'u mu je gida hakanan. Gwadabe Allah ya ƙara sauƙi" "Ameen nagode, ku gaisa gida" Jiki a mace suka fita. Kuɗi ya zaro ya ba Shafa yace ta kai musu Ta fita ta samu Yaya Halima na share hawaye. "Yaya wai gashi Baban Abba yace in baku" Da sauri harda rige_rige wajen karɓar kuɗin Da'u ne yayi nasarar warce kudin. Kwana uku cib basu ɗaura tukunya ba, sai dai abinda aka dafa a gidan aka basu. "Shafa kice mishi mun gode. Me sunan ƴar tamu ne?" Murmusawa Shafa tayi tace. "Sunanta Iyabo" Tare suka sake maimaita sunan. "Iyabo?" Sai suka shiga karkaɗa kai kawai. A wajen dai Shafa ta koma ta barsu. To ana sallamar Gwadabe suka rankaya gidan Bara'u. Gwadabe ya mugun matsantama kanshi sosai. "Gwadabe abinka ya soma zama fa iskanci. Shin ka mance wai Iyabo da mijinta ne? Kafa sauwaƙama kan ka. Ka daure kaci abincin kaga kayi ma Chairman alƙawarin zaka je ku tattauna zuwa bayan isha a gidanshi. Yanzu dai ga abincinnan ka daure kaci sai mu tafi sallah." Ganin ran Bara'u ya ɓaci da yawa ne yasa Gwadabe yayi saurin jawo abincin gabanshi ya soma ci. "Yauwa tsuntsun soyayya ko kaifa. Amman naga jikin naka babu ƙarfi zamu iya tafiya mai nisa gobe kuwa garin fa da bala'in nisa. Ko dai mu bari ka warware da kyau ne?" "A_a Bara'u jikin fa babu laifi. Jirinma ai kaga da sauƙi" Ya faɗa da sauri, tare da ƙara ƙwarara kanshi. Alwala suka yi suka fice masallaci sallar magriba. Ai kuwa ga Gwadabe a sahu ga Da'u. Gabansu kuwa Sukairajune, shi bai ga shigowar Gwadabe ba har sai da aka idar da sallah. Juyowar da zaiyi carab idanunsu ya sarƙe dana juna. Sukairaju yayi tsamo_tsamo sai kallon Gwadabe yake yi ƙaunar ƴan uwantaka na ratsashi. Haƙiƙa suna jin matsananciyar kunyar Gwadabe domin sun san abinda suka yi mishi babu daɗi sun sashi a cikin tsaka mai wuyar fita. Amman dake Allah al hakim ne yau jibi Gwadabe cikin rigar mutunci, su kuwa babu sana'a babu dukiya yanzu ne suka soma daga farko, a yayin da shi kuma Gwadabe likkafarshi taci gaba. Sum_sum Sukairaju ya fice daga Masallacin ba tare daya kula Gwadaben ba. Shima da idanu kaɗai ya bishi har ya fice yana mamakin ramarshi. Da'u dai da zai fita sai da ya sake gaishe da Gwadabe da jiki tare da yin godiyar kuɗin da Shafa ta kawo musu ɗazu kafin ya fita. Zulƙi ne ya matso kusa dasu sukaita hirarsu a ƙoƙarinsu na kawarma da Gwadabe tunaninshi. Suna sallacewa suka nufi gidan Chairman dan tattaunawa. Taron daya haɗa da masu jiran kujerar kansilolin ragowar gundumomin kamar dai Gwadabe suka ga junansu aka gaggaisa nan taron ya soma. "To mu dai fatanmu shine kamar yadda gwamna yace mu zaɓo waɗanda suka cancanta, a namu tunanin mun zaɓo ku. Ya kuma rage naku ku yi abinda har abada tarihi bazai manta daku ba. Ku sani wata amanace ta talakawa zata dawo hannunku. In kuka hau kujerar mulkinnan ku ji tsoron Allah ku yi tsaiwar daka dan ganin kun wakilci Takai wakilci mai kyau" Charman ya jima sosai yana bayaninshi. Kafin ɗays bayan ɗaya ƴan takarar gundumomin suka soma nasu jawabin dalla_dallah. Taron bai watse ba sai da suka yi liyafar cin abinci tukunna. Bara'u dai shi kaɗaine ɗan rakiya yau gashi dalili yayi dalili gashi ga Chairman a zaune a inuwa ɗaya harma yana cin abincin gidanshi. Allah mai iko" Washegari suka ɗauki hanyar Adamawa amman Bara'u ya ba da shawarar Shafa ta zauna ita da Sakina su dai su tafi, dan tafiyar bata rago bace. Suna ta casar tafiya a hanya amman Gwadabe hankalinshi da tunaninshi ma basa jikinshi yayi zurfi sosai. Ina godiya da addu,o'inku a gareni, waɗanda suka kirani a waya ina godiya. Waɗanda suka turo mun saƙo suma ina godiya sosai. Haƙiƙa naga soyayya daga wajen masoyana masu bibiyar rubutana sosai Ubangiji Allah ya bar mana zumuncinmu. Kuyi haƙuri posting zai dawo na dare bana safe ba. Ba wannan tafiyar kaɗaiba duk wata fitowa da zanyi da daddare zan dinga posting kafinnan mata duk sun gama kwaramniyar gida sai su washe ƙwaƙwalensu da karatu ko ya kuka ce masoyana. Nagode sosai. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI **Anty Ramlex Me kayan Da'a,ingantattu,fitattu,kuma shahararru* Na zo muku da albishir na Promo Promo Promo💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽 Abun da kuka Dade Kuna nema....,hakika dogon Jira ya kare.....Ga abunda kuke bege gaba gare ku💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽ba sai kunyi godiya ba menene amfanin zaman tare😌🤫😉 Ina Uwargida me son sabunta martabarta a wurin Oga,Ina amaren bana masu son su mallaki zuciyar ango,Ina zawarawa da suka shirya gyaran abun cikin buje,domin farfado da mutuntakarsu........ku matso kusa...... Hajiya ta sauke farashi,me kike jira........ Babban set na promo ~#20k~#15k👌🏼 🎯 _dambun zabuwa 🎯tsumin bugenta shakaf 🎯Gumbar Madara me Sanya megida Santi da dalalar yawu 🎯Hadin dabino da cukwui hadin basarakiya 🎯Tsugunno me sirri_ *Karamin set*~#15k~#10k💃🏽 📯Herbal for vaginal infection 📯Tsimin bujenta shakaf 📯Gumbar Madara da hadin dabino. 📯Hadin dabino da cukwui (manta uwa) 📯Tsugunno me sirri 🚚Muna aika kaya ko Ina a fadin Nigeria da kewaye. 📞Ku tuntubeni a wnn numbern 07069722234 Anty Ramlex taku ce🥰 MAMA YA DAHU.. ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU (13) TABALBALIN Uwani na turare ɗakinta da turarukan wuta Laure tayo sallama ta shigo da tiran abinci niƙi_niƙi. "Hajiya ga abinci inji Hajiya Babba ta kuma ce tana gaisheki." "Allah sarki kice mata ina amsawa zan shigo inna yi Sallah mu gaisa in ga yaran ma" Laure tace. "Za'a faɗa mata in sha Allah" Ta saka kai ta fita. Bayan Uwani ta bi saƙo da lungun gidanta ta turare ko ina. Sai ta yi sallar magriba kana ta nufi daining table domin cin abincinta kuma. Da Uwani ta buɗe abincin wallahi take ta raina kanta. Tun daga ƙamshin, kama da kyanshi a ido, uwa uba daɗi a baki. Tuwone na semobita da wata iriyar miya wanda Uwani ta rasa gane wacce iriyar miya ce wannan dan ba irin miyar tuwon Arewa bane. Ga wasu irin kifaye sama da kala bakwai a cikin miyar gunduma_gunduma. A baki dai uwani ta gane akwai albasa sosai a miyar, ta ji ƙamshin niƙaƙƙiyar gyada ma. ( Miyar duniya ce wallahi) Ɗayar kular kuma farfesun ƙafar saniyace tayi mugun danƙo sosai ta dahu har kashin ya rabu da nama. Uwani na cin abincinnan tana girgiza kai. Sai da ta ƙoshi ta yi ƙas ta wanke hannu tukunna. Sai ta soma tunanin da sakel ya zame mata dole ta sake zage damtse wajen fito da kalolin girki na ƙasashe daban_daban ba iyakar abinda akeyi a Najeriya ba najeriyar ma Arewa. Murmushi tayi ta miƙe da ƙarfin guiwa data tuno da nau'ikan abincin larabawa da abubbuwan shan su. Mayafi ta zara ta fice duk inda ta gilma sai ƙamshin turaren turara kaya take yi ƙamshin yana tsayawa a duk inda uwani ta ratsa. A matattakalar benen sauka suka ci karo da Hajiya Sa'a suna haurowa ita da ƴan yaranta mata su biyu. Tun daga dai nesa data hango uwani sai ta turɓune rai. Itako Uwani da fara,a tace. "Hajiya Sa'a barka da gidan. Sai naji kamar tsayuwar motar Alhaji Sama'ila ko?" Da mamaki ta dubi Uwanin dan ba'a kiran sunanshi da Abba kab yara da su matanshi suke kiranshi harma da masu gadinshi." "E shine" Tana faɗar haka ta yi wucewarta. Uwani tayi murmushi tare da yin ƙwafa. "Dani kike zancan wallahi in dai nice zuchiyarki ma na dab da bugawa ne. Ni bana ɗaukar iskanci Allah ma ya sani. Mata sai shegen baƙin hali, nifa miji bai dameni ba balle kishiya wallahi " Tana sauka harabar gidan ta hango babbar yarinyar Hajiya Mansa mai suna Mabaruka ta amshi jakar uban. Ƙannenta suna biye da'ita yayin da uban ya take musu baya. Uwargida Hajiya Mansa kuwa tana bakin barandar shashenta tana jiran isowarsu. Tayi ado da wata jar atampa dinkin doguwar rigar daya shanye ƙibarta ya ɓoye tumbinta tayi kyau sosai kamar ba itace uwar zagada zagadan ƴan mata da samarin ba. Murmushi ta sakarma mijinta shima murmushin yayi mata suka shige ciki. Uwani na harɗe tanaa kallonsu cikin sha'awa. Hajiya Sa'a na daga barandar sama itama kallon nasu take yi. Uwani na ɗaga kai ta hangota ita kuma sai karkaɗa kai take tana bin shashen Hajiya Mansa da kallo. Murmusawa Uwani tayi kawai ta nufi shashen Hajiya babba. Da sallama ta shiga du suna falo a baje a ƙasa Alhaji Sama'ila yanata ciro kayayyaki a leda. Ita kuma uwargidan tana ɓarayin daining tana zuba mishi abinci. Tana ganin Uwani ta saki murmushi. "Hajiya Uwani kece? Mu da muke shirin haurowa da yaran duka? Samira ga Antynku ku gaisheta." Murmushi Uwani ta mayar mata ta nemi waje ta zauna, cikin mutunci da girmamawa suka gaishe da Uwani. Alhaji Sama'ila ya sallami ko wannensu da tsaraba kana ya dawo da kallonshi wajen Uwani. "Amarya ba kya laifi. Dama kuwa nayi tunanin in haura wajenki dangane da batun shagonki na kasuwa. Yaran da aka saka aiki sun gama jera komai. Zuwa gobe zan ɗaukeki in kai ki, kiga wajen." Hajiya Mansa ce ta karaso suka gaisa da Uwani tare da yi mata Allah ya sanya alkhairi batun shago. Uwani dai bata jima ba ta miƙe Ai kuwa Hajiya mansa ta ciko mata leda da cincin da alkali na bikin ƙaninta da suka yi. Tayi musu sallama ta fita. Washegari da sassafe ta gama aikinta ta ci ado sosai na kece sara ta sakko ƙasa Alhaji Sama'ila na jiranta su fita. A bakin motarshi ta samu Hajiya Sa'a a tsaye suna magana, da dukkan halamu ƙorafi take yi mishi ko akan menene dai oho. Ganin isowar Uwani ne yasa tayi shiru tare da sake tamke fuskarta. Haɗe rai Uwani tayi bata tankata ba ta ratse ta bayanta. Ita kuma tayi ƙabe_ƙabe a gaban motar. "Baiwar Allah ɗan matsa ko inaso zan shiga motarr." Uwani ta faɗa rai a haɗe. Buɗar bakin Hajiya Sa'a sai tace. "Tunda ni kika zo kika samu ai sai ki jira in gama abinda ya kawonu ko tunda ba kwana zanyi ba. Sannan ko da kika zo kinyi sallamane balle gaisuwa?" Ta yi maganar cike da wulaƙanci. Uwani ta kalleta ta sake kallonta har ƙasa. Sai kawai tayi dariya tace. "Hajiya Sa'a ni dinnan da kika ganni bana neman faɗa, amman fa bana barin ta kwana balle tayi tsami. Na fahimci baki samu tarbiyya ba, ko girman kaine yayi miki yawa, ko kishi ke muƙirƙusarki ohon miki dai. Ai tunda nazo gidannan baki taɓa buɗe baki kin gaisheni ba. Kinga kuwa ai ba zamanki nake yi ba da zanta binki da saƙon gaisuwa sai kace wata ƴar iska ba" Wani dogon tsaki Uwani ta saki tare da jan kafaɗar Hajiya Sa'a zuwa gefe tayi shigewarta mota. Hajiya Sa'a kasa magana tayi dan mamaki. Shi ko Alhaji Sama'ila baice musu komai ba. Ya fahimci Uwani dama zata yi mishi maganin rashin mutuncin Hajiya Sa'a. Ta saba cunkusama Hajiya Mansa baƙaƙen maganganu yau gashi ita ake mayarma. Uwani ba tai aune ba Hajiya Sa'a ta bude murfin motar sai ji kake tas ta mari Uwani tare da karkaɗa yatsunta tace. "Ruwa ba sa'an kwando bane. Iyayena sun fi ƙarfin ki zagesu marar tarbiyya wacce ta je saudiyya ta gama iskancinta da mazan larabawa. Wata uwar tsawa Alhaji Sama'ila ya daka ma Hajiya Sa'a. Uwani ta yinkura zata fita ya riƙeta. "A_a Uwani kinga gidannan cike yake da masu aiki. Ki yi haquri in na dawo da daddare sai muyi magana" Ai bai ƙarasa magana ba Uwani ta fice jikinta har rawa yake yi ta dira a wuyan Hajiya Sa'a. Ba sai dambe ya kaure ba. Uwani ta zage ta dinga jibgar Hajiya Sa'a kamar Allah ne ya aikota. Hajiya Mansa da yaranta da Laure ne suka tawo a guje, suna ƙoƙarin ɓanɓare Uwani a wuyan Hajiya Sa'a. Uwani ta maƙalƙale mata wuya sai gula take mata a ciki da dundu a baya. "Alhaji Sama'ila ka fito ka raba wannan faɗan dan Allah, jini ne yake fita fa. Ku Mabaruka maza kuje direba ya kai ku makaranta " Da sauri yaran suka tafi dan basu taɓa ganin tashin hankali haka ba. Alhaji Sama'ila ne yasa hannu ya ɓanɓare Uwani daga wuyan Hajiya Sa'a, yana tsakiyarsu. "Ke shiga mota mu wuce, ke kuma ki haura sama inna dawo zamu yi magana" "Iyakar abinda zaka ce kenan Alhaji. Jibi abinda mahaukaciyar matarka tayi mun." Ta nuna mishi wuyanta da Uwani duk ta yakushe mata yana jini, ga cikinta a ƙulle. "Mekike so ince dan Allah Hajiya Sa'a. Ba dai juninki bane faɗa da masifa ba. To dama watarana sai ka samu daidai da kai." Hajiya Mansa tace. "A dai yi haƙuri ai Sa'a da hakuri kika yi. Uwani yaushe ta zo gidan da har za'a soma irin wannan abun?" "Dallah malama ki rufa mana baki...." Kafin ta ƙarashe Uwani tayi wuf ta matsar da Alhaji Sama'ila ta sake rarumar Hajiya Sa'a suke tafi taga_taga suka faɗi yib a cikin ciyayi. Uwani ta ɗale ruwan cikin Hajiya Sa'a. An yi abu sosai dan kayan jikinsu duk yayyagewa yayi. Nono Uwani ta riƙe ma Hajiya Sa'a carab, sai ihun azsba take yi. Alhaji Sama'ila ya kama hannun Uwani ya haura da'ita sama ya kulle ɗakin nata. Ya sakko ya koma wajen su Hajiya Sa'a da take ta kumfar bakin ita wallahi ba zata yarda ba. "Kin kyauta Sa'a. Na kuma gode da wulaƙantani da kika yi a gidana. Hajiya Mansa cikata nace" Da sauri Hajiya Mansa ta saketa. Keyn ɗakin Uwani ya bata yace. "Gashi zuwa anjima ki buɗeta. Ke kuma in direba ya dawo daga kai su Samira ya Kai ki asibiti." Ya ja motarshi ya fice. Uwani dan jaraba ta window ta zuro kanta ta nuna su Hajiya Sa'a tace. "Zaki san kin ce mun karuwa. Faɗannan wallahi bai kareba kinsan Allah saina zaneki ciki da waje sannan hankalina zai kwanta. Zan nuna miki ni cikakkiyar ƴar bariki ce" Hajiya Sa'a tace. "Ni an faɗa miki ƙyaleku zanyi ki karyani? Wawuya daƙiƙiya ashe mahaukaciya Alhaji Sama'ila ya auro bamu sani ba" Uwani ta dinga aiko guma_guman zagi ji take yi kamar ta diro daga sama. Hatta maƙota sai da suka shigo. Da ƙyar uwani tayi shiru, shima sai da Hajiya Sa'a ta shiga mota direba ya kaita asibiti bayan ta sake kayane. Uwani ta kai mari ta kai gwauro a falonta sai naushin hannunta take yi tsabar masifa hancinta sai bubbuɗewa yake yi. "Hahaha ai na rantse da Allah saina ɗarsa miki tsorona a zuchiyarki ta yadda ko waje nazo sai dai ki gudu. Bura uba ni kishiya zata yima wannan cin kashin a gaban miji in ƙyaleta? Ai wallahi bata isaba da dai iyabo ce itace lusara matsoraciya." Uwani ta jima sosai tana kai kawo. Sai da tayi wanka ta ɗauro alwala ta dinga nafila kafin jikinta ya dena rawa. Wajajen azahar Hajiya Mansa ta buɗe barayin Uwani Laure ta shigar mata da abincin ranarta. Har zuwa la'asar babu Hajiya Sa'a babu labarinta. Hajiya Mansa ce ta kwankwasa ƙofar falon Uwani. Uwani tazo ta buɗe mata tare da tarbarta da fara 'a. Waje ta samu ta zauna. "Hajiya Uwani ashe kema babu damane wajen faɗa?" Ta ƙarashe zancen da dariya. Uwanin ma dariya kawai tayi mata. "To ayi haƙuri dan Allah abun ya wuce kuma dan Allah kar a sake maimaita hakan dan hankalin mai gidan in ya kai dubu nayi imanin a tashe yake. Gamu da ƴan aiki gamu da maƙota. Dan Allah kar ki sake biye mata dan in Hajiya Sa'a ce zata kuma" Kai Uwani ta gyaɗa a zuchiyarta tace. "Ai ni nafi son ta kuma in koya mata hankali tukunna in yaso daga baya a sasanta. A fili kuma ta ja ajjiyar zuchiya tace "Babu komai Hajiya Mansa komai ya wuce na gode da shawara" Sallama Hajiya Mansa tayi ma Uwani ta fita. Ita dai Uwani har washegari bata fito tsakar gidan ba da daddare Alhaji Sama'ila ya shigo ɓarayinta yayi mata faɗa sosai a ranar taga ɓacin ranshi. Amman da safe da ya shigo su gaisa sai ya sake kamar ma ba shi ba. Cikin soyayya suka yi sallama. Da rana Laure ta shigo da sallamarta ta tsugunna a gaban uwani. "Hajiya kice fa zaki yi girkin rana. Hajiya Sa'a bata dawo ba tun fitarta. Hajiya Mansa kuma ta fita girki shine tace in sanar miki kar yaran makaranta su dawo ba'a gama abinci ba" Murmusawa Uwani tayi tace. "To Shikenan Laure ki soma fere mun doya bara in ƙarashe goge _goge zan gangaro, ki jiƙa mun bushasshen kifi da ruwan zafi da gishiri" Laure ta amsa mata da. "To Hajiya " Ta wuce. Uwani ta ƙalƙale ɗakinta ta bunka mix V.I.P turaren wutanta na Mrs Bukhari ko ina ya ɗauki ƙamshi kafin ta sakko ta samu Laure a kitchen suka yi faten doya da wake da bushasshen kifi. Ta sallami kowa aka ba direba na Alhaji Sama'ila ya kai mishi kasuwa. Da yamma Alhaji Sama'ila ya kirata yace me zata girka ne? "Abincin larabawa na musamman" Dariya yayi yace. "To Shikenan yau zan cika tumbina da kyau ashe" Su ka taɓa hirarsu dai kafin daga bisani suka yi sallama. A ranar Uwani ta zage ta dafa mackuba rice ta larabawa kaji ƴan shila guda uku ta zuba, ko wacce kaza gida biyu kawai aka rabata. Sai kazar Alhaji Sama'ila guda ta ɗaura mishi a saman shinkafar. Ta yi jus na bushasshen inabi da dabino mai ɗan karen daɗi. Zuwa takwas da rabi Alhaji Sama'ila ya shiga ɓarayin Uwani wani sanyin ƙamshi falon yake yi cakuɗe da ƙamshin wannan shinkafa. Idanu ya lumshe ganin uwani yasa gajiyarshi ta soma raguwa. A gurguje ya watso ruwa yazo daining ya tadda uwani ta zuba mishi abinci. Yana ci yana santin wannan shinkafa. Suka jiyo ƙwanƙwasa ƙofa. Uwani ce ta taje ta buɗe ƙofar. Hajiya Sa'a ta gani a tsaye tare da wani dattijo. "Ki mana magana da Alhaji" Ta faɗa rai a haɗe. Murmushi Uwani tayi mata ta dubi wannan dattijo da batasan ko waye ɗinta ba ta gaisheshi kana ta rufe ƙofarta. Ƙarasawa tayi ta zauna bata ce mishi komai ba har sai da ya gama cin abincinshi kafin ta bashi saƙon. "Yanzu kaje ka dawo ina jiranka zanyi ma tausa, gashi nayi maka babban tanadi" Murmushi yayi mata yace. "Bazan jima ba zaki ganni, ke dai ki zauna da shirinki" Fuskarta ya shafa tare da zura malum_malum ɗinshi ya fice. Bayanshi tabi da wata muguwar dariya tace. "Yau Hajiya Sa'a Uwani ta balbalin zata nuna miki ta fiki masifa da bala'i wallahi. Ni da ke shege ka fasa dan uban Mutum. To a wannan dare dai an sha gagarumin rikici a tsakanin Hajiya Sa'a da Tabalbalin Alhaji Sama'ila kuwa yana tsakiya. Duk bala'in Hajiya Sa'a sai taga Uwani ta damata ta shanye. Hajiya Mansa itace ta raba wannan taƙaddamar. "Alhaji tunda dai Hajiya Uwani itace tayi girkin rana dana dare, kuma ka riga da har ka shiga ɗakinta kafin ita Hajiya Sa'a ta dawo. Ni ina ganin ka kwana a ɗakin Hajiya Uwani Allah bashi gobe sai ka koma can din faƙat." Harara Hajiya Sa'a ta sakarma Hajiya Mansa itakuwa a zuchiyarta tana farin ciki sosai da zuwan Uwani wannan gida ko babu komai dole kowa ya kame kanshi danta lura uwani a tsaye take ya maman maza" Gaga gaga haka rayuwar gidan Alhaji Sama'ila ta ci gaba da wakana, Uwani dai sai da ta koya ma Hajiya Sa'a hankali aka hau sama aka rikito aka juya gidan sama a ƙasa , har zaneta sai da Uwani tayi kafin komai ya sassauto suka soma shiri da juna sosai. Ita kuma mai girma uwargida dama tana gefe bata shiga sabgar kowa, ƴar kasuwace kullum tana hanyar Dubai, Uwani kuma na hanyar Saudiya sari. Dukiya sai sake haɓɓaka yake ta yi, wayon da Uwani tayi shine a cikin ribar kuɗin Iyabo da ake juya mata ita da Burodami Debisi sai suke sai mata ƴan ƙananun gidaje haka ana zuba haya ana sake dulmiya kuɗin a kasuwanci. Uwani tayi ƙoƙari dan har aike take yima su Toye a madadin Iyabo, kuma bata rabu da zuwa duba Dada a jaɓɓi lamba ba. Takan baro ƙauyen cikin damuwa da kewar aminiyar arzikinta. Gashi har zuwa lokacin babu labari su Hamma, wanda zai kawo labarin nasu ma babu shi. Wannan kenan" Gaga_gaga haka dai rayuwa taci gaba da wakana. Hafizu yana kawo ma uwani su Ummu Kulsum duk ƙarshen wata su wuni da daddare ya je ya ɗakkosu Alhaji Sama'ila ya ɗauki kuɗi ya bashi yana yaƙe baki yana dariya zai karɓi kudinnan. Uwani kullum a zuchiyarta tana faɗin Allah wadaran naka ya lalace. Rannan kuwa Hafizu ya kawo yara yayi katari Uwani zuchiyarta a sama take. Da Hafizu da yaran duk tace kar su zauna mata a falo. "Wai meye ne nifa Hafizu ka zame mun ƙarfen ƙafa kai da yaranka duka. Na gaji da zuwanku, ina baƙin cikin zuwan da kake yi mun. Dan haka ga hanya ka fice mun, suma su bika. Ke Ummu Kulsum zaki iya gane gidannan ko?" Yarinyar tayi saurin ɗaga kanta haramar e. "To ki dinga riƙo hannun ƙannenki kuna zuwa ku bazan hanaku ba. Amman wallahi hsfizu duk randa na kuma ganinka a gidannan zan sakar maka kare su yo mub farautarka Dariya Hafizu yayi yace. "Haba Uwani me yayi zafi naga duk mun zama ɗaya ni dama in talauci ya doke nine sai in riƙo yaran muzo. Ki daure kar ki yi mun..... Wani kallo da tayi mishi ne yasa yaja bakinshi yayi shiru, ta ja yaran suka nufi hanyar fita. Juyowa yayi yace. "Uwani ko abinci bamu ci ba tun jiya, yarannan an korosu a makaranta, bamu da kudin motar zuwa gida ma. Ki taimaka ko ɗari biyu ce ki bamu" Nera ɗari biyar ta danƙama ƴar tace. "Maza ku je." Haka suka fice. Dole Hafizu ya dena zuwa gidan uwani sai dai yaran. Ashe ya zage ya samu mijin Uwani a kasuwa ya mishi bayanin halin da suke ciki ya bashi buhun shinkafa ya kuma ɗauke nauyin karatun yaran uwani har jami'a. Ai ranar da su Ummu Kulsum suka zo suns ba uwani labari. Har tashar su Hafizu taje tayi mishi biji_biji ta koma gida. Kunji wata jar jaraba fa a wajen Hafizu. Shi bashi da zuchiya dai. Nima nace Allah wadaran naka ya lalace. Mrs Bukhari ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU..... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU 14 Usman bin Usman:. Usman "Allah ya kyauta mata halinsu ai sai su. Bari in shiga in watsa ruwa" "Yaya Amaryar fa to?" Har Usman ya juya ya juyo yace. "Tana can gida taƙi biyoni." Dariya suka yi duka. Ɗakinshi ya wuce yana nan tsab komai a goge a gyare, an sake labule, an sake zanin gado, banɗakin ma daya shiga s gyare yake a wanke yanata ƙamshin sabulun wankin tayil. Yana wanka yana tunanin Iyabo har ya fito tunaninta bai barshi ba. Zama yayi ya goge jikinshi ya ɗan shafa cocobutter dinshi yabi jikinshi da turaren boss. Rigar bacci mai dogon wando ya saka lokacin ƙarfe taran dare yayi. Kanshi ya girgiza kawai ya fito babu kowa a falon wuta da kayan kallon falon a kashe suke. Ɗakin Faisal ya soma buɗewa yana kwance yana danna wayarshi. Murmushi suka sakarma junansu dashi da saurayin ɗan nashi mai tsananin kama dashi. "Ummanku wai tananan kuwa, ni fa ko ɗuriyarta banji ba?" "Abba tananan. Nima tun safe ban sata a idanuna ba, amman su Biba suna tare da'ita." Shiru yayi kawai ya rufe ma yaron ƙofa. Yana tafe yana mamaki har zuwa ɗakin Biba da Abida. Babu kowa a cikin ɗakin kan gadonsu da ƙasa duk kayane harda plate da suka ci abinci a ƙasa. "Wannan yara sai nayi maganinku" Daga ɗakin Suhailat yake jiyo karaɗin Biba, yasan dai Abida tana ɓarayin uwarta dan da wuya ka ganta a ɗakin Suhailat. Yana shiga Suhailat dake kwance tana karanta littafin turanci ta wani haɗe rai da kuma dariya suke yi. Da Biba da Anisa ƙanwar Suhailat suka gaisheshi suna shirin fita Usman yace. "Anisa ni banga su Gaddafi ba tunda na shigo, suna yawon dare ne?" Yayi tambayarne dan son jin ta bakin yaran. Anisa tace. "Su Gaddafi Abba suna Sudan sun koma gida" Kai ya gyaɗa mata kawai hakan yasa suka fita. Sai da suka rufe ƙofar Usman ya dawo da dubanshi gun Suhailat wacce bil hakƙi ta mayar da kanta kan karatun da take yi. Bangon littafin ya dinga kallo yana nanata sunan littafin. Har tsawon minti biyar Suhailat bata saurareshi ba, take ranshi kawai ya ɓaci a zuchiye ya miƙe ya fice tare da doka mata ƙofar ɗakin nata daram kunsan masu suna Usman akwaisu da saurin fishi. A falon ƙasa yaci karo da Asma'u tana sakkowa. Ko kallo bata isheshiba taga yayi sashenshi. Bakinta ta taɓe kawai. A cikin wannan daren Suhailat haka ta kusan raba dare a jikin windo tana kallon tsakar gida ko Usman zai zo ya fice dan yara sun sanar mata shi kaɗai yazo. Ta ɓangaren Asma'u kuwa a kwance take kanta na kallon fankar sama dake bata iska, minti_minti tana sauke ajjiyar zuchiya dan ita tafi Suhailat shaƙa, kuma zatin Iyabo yayi mata tsaye a wuya. Usman kuma bayan ya gama danne_dannen waya, ya kira Iyabo wayarta a kashe sai yabi lafiyar gado nannauyan bacci ya ɗebeshi dama ya kwaso gajiyar aiki ainun kiran sallar asuba ne ya farkar dashi. Wanka yayo ya zura jallabiya ya fice. A dawowa daga masallaci ne yaci karo da Suhailat a falo. "Sannu da shigowa" Tace mishi. Ganin idanun yaranta ne yasa ya tsaya ya amsata, yaranma suka gaisheshi ya amsa musu cike da kulawa. Wucewarshi yayi ciki ya sake faɗawa gado ya shiga aikin bacci. Kamar a mafarki yaji anayi mishi tafiyar tsutsa a bayanshi. Yana buɗe idanu yaga Suhailat a zaune a gefenshi da kayan bacci a jikinta kamar yadda ya wuceta ɗazu a falo. "Bacci ai ya isa haka ango ka fito mu karya ga kumallonka a falo" Murmushi mai fassarori yayi mata. Ya tashi ya zauna a gefenta jikinsu na gugar juna" "Me yasa a wannan karon kika ɗauki al'amarin kishi da zafi? Ai naga ko lokacin da Asma'u ta shigo gidannan baki nuna takai macen da zaki yi kishi da'ita ba, dama ance larabawa kishin masifa gareku, shi yasa ba'a muku kishiya To me Iyabo tayi miki Suhailat da har kikai fishi dani haka, jibi abinda kika yi mun jiya kina ganin kyautuwar hakan amman?" Murmushi tayi tace. "Yadda kake rawar ƙafa akan ita Iyabo, ya bambanta sosai da lokacin aurenka da Asma'u. Auren Asma'u ni kaɗaice akan auren komai ni kaba kuɗin nayi. Saɓanin wannan da Anty Sumayya ka ɗaura akan komai. Aka kawota danginka suka sake nuna mana ita mowar mata ce. Ƙannena ka koresu daga ciki suka koma masaukin baƙi duk akan Iyabo ita kaɗai dame tafi sauran mata to?" Hannunta ya riƙe yana wasa da yatsunta yace. "In banda daru na mata shin dole ne saina ɗauraki akan komaine Suhailat. Kenan ita Anty Sumayya bata da damar yin kane_kane a lamarina alhalin kinsan bani da tamkarta. Oh wannan daliline yasa kika kori su Gaddafi, kika kasa zuwa kiga iyabo?" "Sosai in ganta inyi mata me? Ai tuni an zana mini yadda take. Bana fatan ganinta danni da zaka raba mana gida da'ita da zanfi so. Kaga mu ture batun wannan bazawarar taka muje ka karya ko?" Miƙewa yayi ya shige banɗaki ya wanke bakinshi yana jujjuya maganganun Suhailat. Ko da ya fito bata ɗakin bai fita ba saida ya saka kayanshi. Ƙananun kaya ya saka ya feshe jikinshi da turaren boss ys fito falon ya nemi waje ya zauna Suhailat ta zuba mishi abinci. Ta haɗe rai tayi kicin_kicin yana tura soyayyen dankalin yana ƙare mata kallo yana mamakinta da kishinta yayi tsanani akan Iyabo. A cikin zuchiyarshi yace. "Ku sha kuruminku Iyabo ba zata taɓa zama tare da ku ba tare dani zata zauna ko mun shigo ƙasar zan kaita wani gidan daban. A fili kuma yace" "Ki kira su Gaddafi kice su dawo. Yau zan turo a kwashe kayan Iyabo a ɓarayin, su suyi dawowarsu tunda haka kuke buƙata daga ke har Asma'un" Da sauri ta kalleshi tace. "Ina kuma za'a kai kayan nata to?" Sai da ya gama tauna dankalin ya haɗiye kafin yace. "Gidana dake kusa da Alhaji Baba can za'a kai mata kayan nata sai ya zama gidanta tunda bakya buƙatar a haɗaku hakkinku ne, in kuna so ne za'a iya haɗaku in ɗaya ta nuna bata so dole a raba gida" Jin haka yasa Suhailat ta gane tayi babbar wauta ya daga zuwan wata bare za'a bata gida sukutum kuma gashi mai kyau duk da dai gidan ƙaramine amman zasu sake su sha soyayyarsu. Ai babu shiri tace. "A_a ai bazai yiwu ba. Ka barta anan ƴan uwanta sun riga sun gama mata jere kuma ai anan suka santa" "To Shikenan" Iyakar abinda yace kenan dan bashi da lokacin da mace zata dinga raina mishi wayau haka. Ita kuna a tunaninta ya bar maganar. Sai da ya gama ya fita a gidan. Fitarshi baifi da awa biyu ba sai ga motar diban kaya ta shigo harabar gidan. Suhailat ai saita burkice ta shiga kiran layin Usman amman baya ɗauka. Ta kira Mus'ab ta ari wayarshi ta kira Usman ɗin ringing ɗaya Usman ya ɗaga wayar. "Hello Abban yara. Masu motar kamfanine suka zo wai sun zo diban kaya. Bana baka haƙuri ba ai ba'ayi haka ba kaine fa kace baka son raba kan yaranka ko ka mance?". "Ban mance ba. Aikin gama ya gama na kira su Gaddafi ma suna hanya zasu dawo ɗakinsu. Kiba Mus'ab waya dama zanyi magana dashi" Taso yin magiya amman ya katseta tsaki taja ta miƙama Mus'ab wayarshi ta haura sama bata ko iya gani sosai. Mus'ab ya kara wayar a kunne. "Mus'ab ka biyosu ka nuna musu gidan, nima ina gidan ana kan wankewa. Ai naga gidan baya buƙatar ma fenti ma" Mus'ab ya haɗiye dariyarshi yace. "To Shikenan Yaya sai mun zo ɗin" Ya kashe wayarshi. Hajiya Asma'u ce ta sakko tabi masu diba kaya da idanu sun fita da kujera" "Mus'ab lafiya kuwa ina kuma za'a kai kayan?" "Gidan Yaya dake kusa da Alhaji Baba wannan gidan ginin turawa" A haka ya nufi hanyar waje ya barta tana maimaita gidanshi na kusa da Alhaji Baba? Tsakar gidan ta fito. Matan ƙannen Usman duk sun wani firfito sai ƙus_ƙus suke yi. Da uwar harara ta bisu ta doka tsaki ta shige samanta ta zauna a kan gado ta dafe kanta dake neman tsagewa gida biyu. IYABO:. Ni dai tunda na kwanta bani na farka ba sai asuba. Bayan nayi salla na yi wanka ni da yaran sai na fito taya Luba girkin safe. Da misalin goman safe muna zaune a falo Luba na bani labari Hajiya ta kira Luba a waya akan suna hanyar dawowa dan haka ayi girkin dare dasu. Hakanne yasa nace ma Luba nice zanyi girkin daren. Wajajen azahar sai ga Usman ya shigo sai naga hannunshi duk datti ya nufi masaukina. Barin biyu nayi a wajen Luba nabi bayanshi. Ina shiga yana fitowa daga banɗaki. Idanu muka zuba ma juna. Yana tsaye yaƙi motsawa nima kuma na kasa ƙarasawa gareshi. Hannunshi ya miƙo mun dole ƙanwar naƙi na bi hannun. Ina ƙarasowa ya fisgoni duk girmana ya ɗaura kaina a ƙirjinshi. Idanuna na lumshe kawai inajin yana wasa da inda yafi ɗaukar hankalinshi. Banyi yinƙurin hanashi ba sai taimaka mishi ma da nayi. Abu fa tun daga tsaye sai gamu a zube a ƙasa. Ku dai kunsan komai. Sallamar Luba ce tasa ya zare bakinshi a nawa yana sauke ajjiyar zuchiya. In tashi tsaye ya hanani tashi. In amsa sallamar ni kuma harshena yayi mun nauyi. Da taji shiru dole ta juya ina jiyo kukan biyu. "Kin susutani haka doguwar riga take zama miki a baya? To daga yau kar in kuma ganinki da zani, doguwar riga kawai nake so, so samu irin waɗannan masu santsin. Ki shirya yau zaki tare dan jiya na ƙwaru" Ni wallahi matanka tsoro suke bani" Saida ya shafi wuyana yana wasa da sarƙar dake wuyan yace. "Ki sha kuruminki ai na dawo dake gidana dake jikin wannan, yanzu haka jera miki kayanki akeyi ma" Idanu na zaro, inason tambayar dalili ya hanani wannan damar. "Ki bani abinci inci zan koma inga aikin. Su Alhaji Baba suna hanya fa yau zasu dawo. Abinci naje na kawo mishi yaci ya ƙoshi ya koma can gidan tare da sake jaddadamun yau da ƙirjinshi zanyi matashin kai. Ni kuma har ga Allah nafi son yaje ga matanshi ni maci amarcin namu a can. Ai kuwa da daddare sai ga su Alhaji Baba. Nan na gabatar musu da abinci suna ci harda Usman suna hira, ni dai nayi shiru .Da dai Alhaji Baba yaga dare yayi sai ya dubi Usman yace. "Ya kamata ka ɗauki haramar tafiya kaga dare na yi. Ƴata kema ya kamata kije ki kwanta gobe zaki tashi da shirye_shiryen tafiya" Ai zuruf na miƙe nayi musu sai da safe, Usman kuma sai kashe mun ido yake yi nayi kamar ban gani ba. Sun jima ina jiyo muryarsu kafin daga bisani ya fice ya tafi can wajen matanshi. Washegari na tashi da shirye_shiryen tafiya. Zuwa taran safe Anty Sumayya tazo muka fita, sai a mota take faɗamun da ƴar mai aikinta zamu tafi zata dinga yi mun renon ƴan biyu kuma ta ɗebe mun kewa in Usman zai yi aikin kwana. Ai kuwa naji daɗi sosai. Shagon dogayen riguna Anty Sumayya ta kaini ta dinga zaɓamun masu kyau kalar ƴan gayu. Daga nan muka shiga shagon rigunan bacci nanma ta siya mun masu bayyana sura ni dai duk kunya ta kamani. Anty Sumayya inaso in sai kaji inaso in yi dambun namane" "To Shikenan akwai mai kajin su Hajiya sai a sa ya kawo" Ai kuwa muna dawowa na samu mai kaji ya kawo guda shida. Ni da Luba muka yi aikin dambun mune har taran dare bamu gama ba. Da daddare sai ga Mus'ab ƙanin Usman da wata ƴar yarinya da bata wuce shekaru sha uku ba da jakar kayanta. Luba ta kirani muka gaisa da Mus'ab yace. "Anty Sumayya ce tace in kawo miki Halima ta kwana sabida gobe sassafe zaku wuce" Allah sarki to nagode sosai ka gaida iyalan" "Zasu ji. Ohh su Halima an zama ƴan India iye iye" Ya shiga tsokanarta ita kuma ta shiga murna. A wannan daren na kai kusan biyun dare ina haɗa kaya. Inayi muna waya da Usman da duk ya dameni da zantukan sake layi. Ni dai sai dariya kawai nake yi mishi. Washegari sassafe Mus'ab yazo shi da Usman shi zai kaimu Airport. Alhaji Baba ya jima yana mun nasiha haka Hajiya ma. Nan nayi sallama da Luba muka kama hanyar Airport. Muna zuwa muka soma bin layin shiga Bus ɗin da zata ƙarasa damu wajen jirgi. Usman na rungume da Hassan ga akwatin kaya. Ni kuma ina riƙe da kayayyaki Halima na goye da usaini. Gaga gaga sai ga jirginmu a Abuja. Hotel ya kama mana a Abuja dan sai dare jirginmu ya ɗaga zuwa India da misalin ƙarfe takwas na dare. Allahu Akbar Allah shi ke da iko akan komai. Tafiyar awa goma sha uku da minti goma a sama. Karfe taran safe jirginmu ya sauka a filin jirgin Rajiv gandhi international airport. Ni dai sai zazzare idanuna nake yi, ina biye da Usman har zuwa fitowarma daga cikin Airport niƙi_niƙi da kaya ga biyu ga Halima. Mota mai ƙafa uku muka shiga wanda a wannan lokacin ban taɓa ganinta ba har ga Allah. A filin jirgin ƙasa motarnan mai ƙafa uku ta sauke mu muka shiga, a wani dogon benci da masu jiran tashin jirgi suke zaune Usman ya zaunar damu. "Ku zauna ina zuwa, zan kawo muku abinci kuci, sai in siyo mana tikiti jirginma da halama ya kusan cika" Ni dai sai zazzare idanu nake yi ina kallo indiyawa maza da mata da yadda suke magana suna motsi da kayukansu. Wasu suna zaune suna cin abinci, duk masu cin abinci abun mamaki da hannu suke ci. Muma Usman ya kawo mana wata shinkafa da kaza, da wasu miyoyi dil_ɗil daban daban kusan kala shida kuma a ganye aka zuba abinci sai aka ɗaura a tire. Ruwa ya zuba mun na wanke bakina da hannayena na soma cin abincin shi yana riƙe da biyu. Halima ma sai zuba loma take yi ta shawo yunwa duk da mun cicci abinci a jirgi amman dangin fulawane kuma ƴan kaɗan kaɗan ne a cikin kwalin. Sai da na ƙoshi na ba biyu suka ci Usman dai yace shi bazai ci ba. Sai da mu ka yi sallar azahar aka soma sanarwa a shiga jirgi. Duk muka shiga muka zazzauna jirgin akwai girma sosai tarago_tarago. Tafiya mabuɗin ilimi muna tafe Usman yana yi mun bayanin garuruwan da muke ta wuwwucewa, abubuwan gwanin sha'awa sai gamu a garin Rajasthan garine mai matuƙar girma da yawan jama'a yana daga cikin manyan birene a India a ƙarƙashin Rajasthan akwai birane masu yawa. Daga nan muka hau wata doguwar bus zuwa Udaipur city. A wannan gari Usman yake zaune. Bamu muka shiga gida ba sai dare, iyakar galabaita nayi sosai abinka da ba'a sababa. Da ƙyar na daure na tashi na yima biyu wanka suka sha nono sai bacci suma sun galabaita sosai. Usman na fitowa daga wanka nima na shiga na watsa ruwa na gargass jikina sosai. A zaune a kan teburi na fito na sameshi yana cin cake da dambun nama da tea. Murmushi ya sakarmun yanata ƙaremun kallo ganina ɗaure da tawul. Ni kuma duk sai naji na takura rigar baccina na dauƙa na koma bayan gida na saka, na shafe jikina da Humrar matan aure. Na fito na sameshi sai dariya yake yi mun ni kuwa na basar na je na ja kujera na zauna na soma shan tean da ya haɗa mun. "Iyakar abinda zaka ci kenan ko in shiga kitchen in dafa maka wani abun?" Idanu ya lumshe yace. "Ya'isheni yau ba daren cika ciki bane yau ni dake ne a wannan daren. Na kai ƴan biyu can ɗakin Halima in muka gama abinda zamu yi sai in dawo dasu, gobe zamu shiga kasuwa mu siyo musu gadon yara" Gaga_gaga a wannan daren abubbuwa da dama sun faru na farin ciki masu tsaiwa a zuchia. Allahu Akbar bawa bai isa tsallake ƙaddara ba, face adda'a dake rage karfin ƙaddara koma ta canjata baki ɗaya. A hakanma nayi imanin adda'ata ita tasa Allah ya taimakeni. Usman ya zame mun uwa ya zame mun uba. Ya haɗani da yara ya rungumemu. Gaga_gaga rayuwa taci gaba da shurawa cikin farin ciki. Cikin watanni dani da ƴan biyu duk muka canja jin daɗi da hutu ya soma sauka sossi a jikinmu. Rayuwar tayi daɗi ci gaba ya sameni na komawa makaranta. Bayan wasu shekaru:. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU 17 INDIA IYABO:. A kwance nake a ɗaki idanuna a lumshe, bayana kamar zai dare gida biyu dan azaba. Tun cikin dare ciwon bayannan ya tashi mun dan ko runtsawa ban ba. Ban kira Usman na sanar mishi ba gudun kar ya baro aikinshi na dare ya dawo gida. Hassan ne ya shigo da gudu ya faɗo kaina. "Umma kinga Alhaji ƙarami yana mun gwalo ko?" Da ƙyar na buɗe idanuna na dubeshi. Wai baka ga Rumaisa'u na bacci bane so kake ka tasheta kai da baka da girma, yanzu Alhaji ƙaramin ka kawo ƙara, ina Halima ta barku kuna wasan banza?" Kafin ya bani amsa Nana ta shigo hannunta riƙe da kofin tea yarinyace ƴar hekara uku ƙanwar Alhaji ƙaramice, yayar Rumaisa'u kuma. "Umma abinci zanci" Hassan yi maza ka kirawo mun Halima yanzu." Na dubi Nana nace. Bari Halima tazo ta baki abincin, ku da in ba makaranta kuka tafi ba bakwa barin mutum ya huta Kafin in rufe bakina sai ga Halima ita da Usaini da Hassan" "Anty gani. Naga har yanzu baki fito ba. Kuma Abba ya kusan dawowa." Agogon dake manne a bangon ɗakin na kalla ƙarfe takwas na safe. Kiba Nana abinci, ki ɗauki Rumaisa'u da su Hassan kuje can ɗakinku ku Zauna bana jin daɗine zasui ta damuna." Ina gama faɗa mata hakan na miƙe da dabara na shiga kitchen. Dankalin turawa Halima ta fere ta tsane a kwalanda shine abincin mu na karyawa yau dake manne a taswurar girkin gidana. Mai na ɗaura a wuta na zuba dankalin. Na sake ɗaura ƙaramar tukunya na haɗa kayan chai tea na jama'ar india. Na gama zuba komai a kula kenan na jiyo sallamar Abban yara a falo, tare da hayaniyar yaran sunata mishi oyoyo. Ni dai ina tsugunne bayana ya kage nama kasa ɗagowa balle har in fito. A haka ya shigo ya sameni yana sanye da lap kot ɗinshi ta likitoci. "Subhanallaah Habibty lafiya na ganki a haka?" Ya faɗa cike da kulawa da tsantsar damuwa. Tallafoni yayi jikinshi da ƙyar muka karasa ciki. Baku tambayeni ƙiba ba hahaha ƙiba sai abinda ya ƙaru akan na da hutu da gogewar rayuwa yasa na zama kyakkyawa sosai. A bakin gadon ɗakinshi ya zaunar dani. "Meke damunku haka, ai ni na ɗauka ma zamu haɗu a asibiti har ward ɗinku na je ƙawarki Sabitri tace mun baki zo ba, kuma ta kira wayarki a kashe. Ba morning kike dashi bane?" Duk wannan maganar da yake yi mun hidima yake yi dani, ya kwantar dani, ya samun fullo ta bayana kamar yadda yake yi mini a duk sanda wannan ƙaddara ta ciwon baya ta tasanmu. Duk bincike, da kwarewa ta likitocin india, da irin kayan aikin da suke dashi wallahi sun kasa samo maganin ciwon bayannan nawa, hoto babu irin wanda ba'ayiba ba'a ganin komai, magani ko nasha sai dai ya lafar da ciwon. In kuwa cikine dani bana iya moruwa wannan dalilinne yasa Usman yasa aka juya mun mahaifar tunda muna da yara biyar ai sun ishemu. "Sannu kinji, amman me yasa baki kirani ba, kuma kika wani shiga kitchen kina haɗa kayan kari. Ai da kin barshi ko tea inna dawo sai in dafa mana ba, ko girkin kike so ba inayi muku ba?." Miƙewa yayi ya ɗakko man zafin da in ciwon ya tashi ake mun masach dashi ya shiga yi mun masach ɗinnan. A kife fuskata take kafin ya gama mun na jiƙe fulo sharab da hawaye. Azabar tana da yawa ainun. Wayata ce tayi ruri a gefen gado. "Ga Hajja Mama na kiranki, bari in ɗauka nasan ba lallai ki iya magana ba" Kai kawai na ɗaga mishi. "Hello Hajja Mama barka da safiya" Daga cikin wayar tace. "Likita bokan turai. Ya gida, ya jikokin nawa?" Murmushi yayi yace. "Suna can ɓarayinsu ai da suna jin na ambaci sunanki zasu soma ihu dake uwar ba lafiya wallahi nima yanzu dawowata daga aiki kenan, ita ko aikin ma ba zata samu zuwa ba" "Assha wannan ciwon baya sai adda'a kawai. Anyi na asibitin, anyi na hausan abu yaƙi ci yaƙi cinyewa. Sai dai muce Allah ya dubeta ya bata lafiya kawai. Kai wannan yarinya tana ibadar Allah. Dama tsintsiyar ƙamshine (turaren wuta ɗan tsinke) masu shaguna suka soma sanarwa yayi ƙasa shine nace bari in kira in sanar mata, to ashe ita babu lafiya ma." Usman yace. "Babu damuwa ai ko Halima sai ta je ta saro tunda tare suke zuwa. Kin turo sunayen waɗanda kuke sonne?" "Na turo likita bokan turai. Muna godiya sosai da irin gudunmawar da kake bama Iyabo, dama mu kanmu mungode ƙwarai Allah ya barku tare har ƙarshen rsyuwarku. Jiya take sanar dani zaku sake zuwa Umara nace baka gajiya ne?" Dariya kawai yayi yace. "Sabida ciwon bayannan nata ne shi yasa nake yawan kaita ka'aba tana roƙon Allah ya yaye mata, in kuma bana warkewa bane Allah yasa shine silar shiganta aljanna. Irin na mata mai farfadiya da ma'aikin Allah ya shaida mata wannan ciwon shine silar shiganta aljanna" Sun ɗan jima suna tattaunawa. Kafin su kai sallama ya ajjiye wayar. Idanuna a lumshe suke amman ba bacci nake yi ba. Ji nayi ya fita, bai jima ba ya dawo da abinci da tea. "Taso kici abinci sai ki sha magani ki kwanta. Zan kira asibitin da kaina in sanar musu baki da lafiya." Sai da ya taimaka mun na samu na iya zama na jingina bayana a kan gadon. A hankali nake cin abincin mu na ɗan taɓa hira, duk da rabi da kwatan hirar ƙorafine akan ban kirashi a waya na sanar mishi ba. Matarshi data kirashi a waya ne ta ceceni ya fita amsa wayar. Sabida karamcinshi baya iya amsa wayar matarshi a gaban ɗayar matar tashi. Asma'u uwar kishi da raina ɗan adam kenan. Na rasa dalilin da yasa matan Usman suke kishina haka. Akan zamana tare dashi a nan da komawata makaranta an sha artabu dasu sosai da sosai, Alhaji Baba ne yake taka musu birki. Dan a baya babu irin magiya da rarrashin da bai yi musu ba akan su bishi su dukka su dawo can da zama sabida suntirin yayi yawa. Ko wacce ta nuna ita tafi son aikinta ba zata iya tafiya ta bar aikinta ba. Ko zuwan da suke yi in anzo da ɗaya azo da ɗaya da ƴar suka yarda shima a cikin ɓacin rai suke yi. Ni sai daga baya ne yake bani labarin komai da zama yayi zama, ya kuma bani labarinshi tun daga ƙuruciya har girmanshi, da rasuwar mahaifiyarsu. Alhaji Baba ma yace duk su tawo Indian tare da yaran nasu. Sai suka nuna su sai dai ni in dawo duk mu hadu mu zauna shine abinda suke so. Irin muguntarnan ta mata na ɗabi'ar kowa ya rasa. Shi kuma Usman ya nuna baisan wannan ba. Shikenan al'amuran gidanshi suka rincaɓe. Duk haihuwa biyu da nayi a can Gombe nake yin wankan jego a gidana. Haihuwar Alhaji ƙarami dukkansu basu zo sun ga yaro ba, sai dai a waya da sukai mun barka. Inata saka idanu inga ranar suna zasu zo ayi hidimar komai dasu, nanma shiru. Hajja Mama ta tambayeni ko sunzo barka na faɗa mata basu zo ba. Nima kuma da yace mun inje bayan suna a lokacin muna shirin komowa nace mai bazan je ba. Ya tambayeni dalili na faɗa mishi. Dan yasan bana musu dashi, bani da fitina akan kishi. A gaskiya ya ɓatar musu sosai ya ci musu. Haka muka dawo India ban sake shiga Najeriya ba. To a Umara na soma ganin hajiya Suhailat taje daga najeriya nima munje daga india, naga kishi irinna mata dan so tayi ita ta kwace mijin acan. Nima anan sai na botsare nace bansan wannan zance ba, dole haka aka shiga rabon kwana a hotel kunji wani kudurar Allah fa. Naga kishi, naga makirci iri da kala, kunsan larabawa akwaisu da wata baƙar zuchiya akan kishin abinda suke so. Ga Iyabo kuma da son soyayya nima. Gaga gaga muka gama ibada tayo Najeriya muma muka koma India To haihuwata ta biyu dai dasu akai taron suna sunzo. Haihuwata ta uku kuma ni banje ba zamana nayi kawai anan. Wannan tsawon lokacin sau biyu rak na taɓa saka matanshi a idanuna. Bayan ya gama wayarshi ya shigo da nashi abincin yana ci muna hira shine yake sanar dani Hajiya Asma'u zata je umara itama zamu haɗu acan. Murmushi nayi nace Allah dai ya nuna mana, babu damuwa " A baya ya bani labarin mahaifiyarshi margayiya. Ya bani labarin gabaki ɗaya kab rayuwarshi. A wannan lokacin ni kaina naso ace ina da ɗan labarin da zan tsokata mishi amman ina, ƙwaƙwalwata a juye take bata iya gane komai bana fahimtar komai. Kwanana biyu a gida a rana ta uku na koma bakin aikiba a asibiti ni nurse ce ba likita ba. Bayan wata ɗaya muka wuce Umara yaran muka kaisu gidan Mus'ab da aikinshi yake Tamil. A Umara Hajiya Asma'u ta so kwata mun irin na Hajiya Suhailat ni kuma nace ba za'ayi haka ba ni naci girman ita ta riƙe mijin Hakan kuwa akayi kwananmu goma sha biyu jirginmu ya ɗaga, dole ƙanwar naƙi itama ta wuce Najeriya. Muna dawowa muka ci gaba da aikinmu dake asibiti ɗaya muke aiki a nan Geetanjali hospital Rajasthan, ɗayane daga cikin manya manyan asibiticin da ake ji dasu a fadin duniya ma. Wannan abun ma yana sake takaitar kishiyoyina Ku dai rayuwa tai ta garawa tana murtsuwakawa. Wata rana kwatsam sai ga kira daga Najeriya Allah ya amshi ran Alhaji Baba Allahu Akbar. Iya tashin hankali Usman ya shiga dan wata iriyar shakuwace ta musamman a tsakaninsu, kasancewar shima yana son su sosai, kuma soyayyar da yake ma mahaifiyarsu itac kacokan ta dawo kansu. Nice na dinga tausarshi da bashi kalma. Ai kuwa nan muka shirya tafiya, sai ranar uku muka iso a nan gidan Alhaji Baba muka sauka dan ko buɗe gidana ni banyi ba. Muka shiga karɓar gaisuwa, baƙi sukaita shigowa daga gari _gari dan familynsu Family ne mai girman gaske. Ina zaune a cikin mata Hassan ya shigo a lokacin shekararshi goma sha bakwai sun riga da sun gansame yana aji na biyu a jami'a kasancewar karatunsu nacan ya bambamta dana gida Najeriya." "Umma Abba yace wai kizo ki sameshi a waje." Yayi mun raɗa a kunnena. Hajja Mama ta jawoshi tace dashi. "Ka je ka kirawo mun Nana ja'ira tunda ta fitar mun da waya ban sake ganinta ba. Ni dai miƙewa nayi da ƙyar sabida ƙiba danma ina motsa jiki sosai babu kasala a tare dani, dan wuni nake yi zirga_zirga a asibiti. Matan gidan na ratse na nufi hanyar waje. Wasu mata da suka shigo na bangaji ɗaya a cikinsu, kaina na juye ina kora Nana cikin gida tana son zata bini. Ita wai dole zata yi magana da Abbansu. Da sauri na juyi. Subhanallaah dan Allah baiwar Allah kiyi haƙuri " Na sa kai zan wuce naji ta riƙo hannuna. "Iyabo wai ko ba ke bace, duk da dai Iyabo bata kai farin haka ba, kuma ƙibarta ba haka ba" Na dubi wannan mata na maya. Baiwar Allah sunana Iyabo. Amman ban wayeki ba. "Allahu Akbar Iyabo Uwani Tabalbalin ce ƙawarki. Dama kina raye baki mutu ba. Tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai." Usman ne ya shigo gidan. A lokacin ni kuma kaina ne yake jujjuya mun, sunan Uwani Tabalbalin yana ta mun amsa kuwa kawai. Abubbuwa suka shiga hasko kansu a ƙwaƙwalwata, lokacin da na baro Jaɓɓi lamba afujajan da goyo nake hangowa ina tafe ina waige. Rayuwar da muke yi da Usman sai sake hasko mun yake yi, Yaya Hamma na tuno, da ƴan biyu na. Ba shiri na runtse idanuna kaina kuwa kamar zai tarwatse dan nauyi. "Ko itace ƙawarki da kike bamu labarin ɓatanta?" Cewar Hajiya Mansa kenan. Itace kimanin shekaru goma sha bakwai da ɓatanta" Kar ku daɗa kar ku raga. Sai na soma hango sanda na goya ƴan biyun yarana a baya na fice cikin dare. Da furucin da Hama ta yi akan saina bar Jaɓɓi lamba a haukace tsirara ma. Ina buɗe idanuna na gane Uwani. Hannuna yana rawa na nunata Tabalbalin kece. Na shiga uku me yasa to na sake wani auren bayan Hamma ne mijina?....." Ban sake sanin kaina ba ashe sunewa nayi ni. Ban tashi farkawa ba sai biyun dare na buɗe idanuna na ganni a ɗakina a kwance ga ƙarin ruwa a hannuna. A wannan sumar ƙwaƙwalwata ta shiga saiti, tare da tariyomun duk rayuwata ta baya. Da ma wanda na gudanar bayan barina jaɓɓi lamba. Hakan yasa a mugun firgice na farka. Uwani, da Hajja Mama, da Usman duk suna kaina. Da uwani muka haɗa idanu ina hawaye, na dubi Usman shima ni yake kallo, wallahi idanunshi yadda kuka san an zuba jini dan tsabar ja, hatta fuskarshi ta koma jawur sai jijiyoyi raɗa_raɗa Ai sai na fashe da kuka kawai ina salati, hankalina ya dawo jikina, kuma wata ƙudura ta Allah, duk rayuwar auren da mu ka yi da Usman yana kaina bai goge ba. Ina Hamma uwani, ina Dada?" Da sauri suka yo kaina nayi sauri na runtse idanuna jin ƙamshin turaren Usman a kusa dani. "Iyabo Hamma yananan a iya tsawon shekaru goma sha bakwai da ɓatanki babu abinda ya sauya na dangane da sonki a zuchiyarshi, har yanzu yananan bai yi aure ba. A kullum adda,arshi Allah ya bayyanaku ke da yaranshi. Ashe wani babbar ƙaddarace ta aure da ƴaƴa ya fitar dake Iyabo. Yau gaki da auren Usman kina a matsayin matar Hamma." "Hasbunallah. Astagrifulla" Muka ji Usman yana ta nanatawa. Tare da shassheƙar kuka na tashin hankali kamar wani ƙaramin yaro. Hajja Mama kuma sai ambaton "Kaico_kaico take yi. Hankalinta har yafi namu ma tashi wallahi. Da ƙyar na buɗe idanuna da su kai mun nauyi, zuchiyata sai dakawa take yi, a halin yanzu babu mahalukin da yake bani tausayi sama da Usman. So zuntsuritunshi wallahi ina yi mishi dan yayi mun dukkan halacci. Tattaunawa yake yi yana shirin fita. Uwani taje da sauri ta taroshi. "Usman kar kaje ko ina. A halin yanzu Iyabo tana buƙatarka fiye da kowa. Dukka wannan abun wata aya Ubangiji ya saukar in mun gane. Usman kayi ma Allah ka dawo ka zauna" Ruwan dake hannuna na zare na sakko, ko kafa ban ɗaga ba na faɗi yib. A zabure Usman ya juyo ya tallafoni zuwa jikinshi. Wata iriyar ƙanƙama nayi mishi ta haƙiƙa. Kallona yake yi hawayena na jiƙa ƙirjinshi. Wata dariya yayi, mai haɗe da kuka lokaci guda. In sakeshi wallahi na kasa, shima ya sake ni ya kasa. Uwani ce tazo ta riƙo hannuna na tashi da ƙyar, a lokacin hannuna sai zubar da jini yake yi ashe harya ɓata ƙasa da jikin Usman. Da sauri ya fice a ɗakin yana fita na lumshe idanuna ina rera nawa kukan. "Ohh Allah. Iyabo ki yafe mun haƙiƙa banyi aiki da tunani ba, idanuna ya rufe burina kawai ki auri Usman. Ashe ke da aure a kanki ban sani ba. Allah na tuba." Likita ce ta shigo ɗakin ta mayar mun da ruwan dana zare. A lokacin jikina yayi wani irin mugun zafi, kaina da idona ciwo kawai suke yi mini. Idanuna na lumshe ina tuno rabuwata da Hamma na ƙarshe a lokacin zasu tafi ciranin kiwo. Wasu zafafan hawaye suka sulalomun Na sake tuno lokacin da nake da cikin Alhaji ƙarami. Irin laulayin da nayi, da irin yadda nake wanke Usman da amai, da wahalar da yasha. Da kuɗi daya kashe ya bani ilimi, ya saka yara a makaranta mai daraja. Da ƙyar na buɗe idanu na dubi Uwani da hajja da duk suka ruɗe sai sannu suke yi mun Murmushin dole nayi musu kawai. Usman yana fita falo ya samu yaran sun yi shiru, Nana tana kusa da Usaini a zaune. Hassan yana tsakiyar Alhaji ƙarami, da Rumaisa'u Kallon yaran kaɗai yayi zuchiyarshi ta sake rugujewa, har yake jin jiri na neman kayar dashi. Ƴan biyu ya kalla Allah shine shaida yana musu so marar misali yayi imani ko ubansu bai isa ya nuna musu so haka ba. Yana da buri sosai akan yaran. Ashe har Iyabo zata iya ɓoye mishi cewar bata iya tuno komai na bayan rayuwarta, ashe tana ɓoye mishi wani abun? Da ta fito ta faɗa mishi gaskiyar lamari ƙila da abinda ya faru ba lallai ya farun ba. Yanzu Yaya zaiyi da rayuwarshi ya akeso yayo?" Da sauri yaran suka nufoshi. "Abba umma ta farka ne, tun ɗazu su Nana suke damunmu akan suna so su ga umma." Da ƙyar yabuɗe baki. "Umma jikinta da sauƙi. Yanzu fa kusan ukun dare ne, Nana kuje ku kwanta da safe inta tashi sai ku dubata. Husaini kuje ku kwanta Allah yayi muku albarka" Yaran suka wuce sum_sum matan suka wuce ɗakinsu mazan ma haka. Usman kuwa zama yayi a falon yana tariyo irin rayuwar farin cikin da suke gudanarwa da Iyabo. Lokaci ɗaya faraɗ ɗaya komai ya damalmale ya canja. Wayarshi ce tayi ruri a karo na barkate. Yasan bazai wuce Suhailat ba, dan a wajenta yau yake. Miƙewa yayi tare da soma zagaye falon yana tunanin abubuwa da dama. Zuchiyarshi da ruhinshi sunyi ƙunci da rauni sosai. Da girmanshi da gemunshi sai hawaye yake zubarwa. A lokacin shekararshi kusan saba'in fa, har jikoki da surukai gareshi amman yau gashi so ya dimautashi yana shirin haukatashi. Banɗakin falon ya shiga ya ɗauro alwala ya zo ya shiga zuba nafila. Iyabo:. Ƙarfe uku da arba'in na dubi Uwani dake riƙe da tea. "Iyabo ki daure ko babu yawa ki sha. Kinga abinda zai faru ya riga da ya faru. Gode ma Allah ya kamata muyi da Allah ya nufa kika dawo cikin hayyacinki ma. Duk da aure kan auren da kika yi bisa rashin sani naji daɗin yadda naga rayuwarki tayi kyau. Nayi imani ba haka akaso ki kasance ba. Haukacewa Hama taso kiyi yaranma ki watsar ku watse rayuwarku ta tarwatse. To ba haka Allah ya tsara ba. Na san kina cikin tsaka mai wuyar fita Iyabo. Amman hakan baya nufin zaki kashe kanki ita ƙaddara ta riga fata da tawakkali na sanki Iyabo" Ajjiyar zuchiya na sauke na karɓi tean ina kurɓarshi tamkar maɗaki dan tsabar ɗaci. Uwani ya Dada take?" "Allah sarki Jabu ta Dada. Dada tananan da ranta cikin ƙoshin ma lafiya. Duk da tasha matsananciyar jinyar rashinki. Amman tsufa sosai ya durar mata Nan uwani ta shiga bani labarin bayan rabuwa. Komai sai da ta labarta mun. Banda gidajen da ta dinga siya mun da kudi da take juyawa. "Hamma yana Sokoto da zama yana kasuwancinshi, baki ganshi ba ya goge ya murje sai dai damuwar rasaku har yanzu ya kasa Aure." Baɗɗo kuwa ta zama uwar mata sai haihuwa take yi. Cubu tana Aure a Adamawa , Usman kuma da Amaduyal suna tare da Dada da matayensu da yara. Abubbuwa da yawa sun faffaru iyabo shekaru kinga ai sun ja da yawa. Murmushi nayi kwaɗayin son ganin Dadana da ƴan uwana ya shigeni. Na gode Allah da yasa Dada bata mutu ba tana raye. Kefa rayuwarki ina su Kulsum da Hafizu?" "Zaki yi saɓo waye kuma Hafizu ni Uwani? Ai ke da ganin zubin kinsan ba kiwon Hafizu bane. Nayi Aure a babban gida ina Auren Alhaji Sama'ila harda yaran mu biyu. Shine ma silar zuwanmu ta'aziyyar da bazan taɓa mancewa ba abadan. Harda kishiyata muka tawo suna hotel gobe ma zasu koma, ni zai barni a wajenki. Kursum kuma tayi aure ciki ne ma da'ita. Zuwa gobe zan samu Usman muyi magana sai muji yadda za'a tsara tafiyarki gida da makomar auren naku." Ina kuka na kwashe kab rayuwar da nayi bayan baro gida na labartama Uwani. "Danƙari narantse da Allah Iyabo dole ki shiga ruɗani, dole kiyi kuka. A tsakanin Gwadabe, Hamma bazan ɓoye miki ba babu wanda ya soki rabin son da Usman yake yi miki. Kai Iyabo gaskiya in Shari'a ta tabbatar da gidan Hamma zaki koma to kinyi rashin masoyi mara madadi. In kuwa shine zai ci gaba da zama mijinki na miki murna" Da sauri na kalleta ina share hawayena. MRS BUKHARI Tofa tashin hankali. Wallahi hannuna har rawa yake yi. Ina typing ina hawaye, Usman ya bani matuƙar tausayi. Sai Allah ya kaimu monday kuma inda a satin zamu ƙarƙare wannan littafi da izinin Allah, komai yazo ƙarshe. Ki faɗi irin darasi ɗaya tak da kika ɗauka a cikin rayuwar iyabo. Domin darusan suna da yawa. Menene ra'ayinku akan labarinnan? ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba.... Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya... ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji? Rashin dandano ko ni'ima? Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa? Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya? Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani ramlex266: 07069722234 ko 08064421211 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 Wannan shafin naku ne ku kaɗai Ramlex mai jego ta amana. Kwamishiniyar buje. Ta kuma masoyiya Mrs Bash ( uwargida a gidan mai ba da shinkafa ƴar gwamnati) Alkhairin Allah ya kai muku NAMA YA DAHU,.... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 18 IYABO:. Wallahi ni Uwani kaina a kulle yake. Kinsan Allah ji nake dama mutuwa nayi tun farko" Hajja Mama wacce duk hirarmu tana zaune tana jinmu tace. "Assha iyabo. Bawa bai isa ya tsallake ƙaddararshi ba, karma ki soma faɗin haka. Dole za'a samu manyan malamai, ko kotun musulunci sune suke da ilimin warware wannan ƙullin. Duk abinda ya faru ki rungumi ƙaddararki. Ki gode ma Allah ma, a jikin Usman gidaje biyu manya kika siya a garin Lagos banda kwala_gwalai da kika tara. Bugu da ƙari kin koma makaranta ke malamar kiwon lafiya ce. Ga yaranki sun samu karatu me kyau. Ki gode ma Allah a duk yadda rayuwa tazo miki " Sukaita rarrashina dani dasu, da Usman ɗina babu wanda ya runtsa a wannan daren. Ruwan hannuna sai asuba ya ƙare na zare na miƙe da taimakon Uwani na ɗauro alwala nayi Sallah ina zaune a kan dadduma na buga tagumi zuchiyata sai harbawa take yi tunanin Usman cakuɗe da tunanin Hamma yana shirin haukata ƙwaƙwalwata. Sallamar su Hassan da Abbansu ne yasa na runtse idanuna zuchiyata kamar zata faso ƙirjina ta faɗo. "Umma ina kwana Yaya jikin naki?" Cewar yaran da suka haɗa bakinsu duk suka zube a gabana Lafiya lau jiki dai to ku yi ta mun adda'a Allah zai kawo mafita kunji ko yaran ummu?" Da wani irin rauni na faɗa to Husaini sun riga sun girma tuni suka fahimci akwai matsala , sai dai basu ga fuskar tambayata ba. A sanyaye muka gaisa da Usman kaina a ƙasa. Muryarshi a dashe ya amsa mun suka gaisa dasu uwani da Hajja Mama ma "Uwani muyi magana dake a falo mana" Ya faɗa yana fita. Miƙewa Uwani tayi suka fito falo A falon Uwani ta tarar da yar Usman ɗin a zaune tana cike da damuwa Anty Sumayya. Gaisawa suka yi da Uwani. "Dan Allah a taƙaice ki bamu labarin iyabo Uwani. Tunda tun kuna yara kuke tare. Inason sanin wacece ita da musabbabin shigarta wannan matsalar da ƙaddara ta cillota garemu" Cewar Anty Sumayya kenan. Uwani nan ta warware musu zare da abawa ta basu labarin duk wata rayuwa ta Iyabo. Kai Usman yake ta kaɗawa ya kasa cewa uffan sai tsananin so cakuɗe da tausayin rayuwar matarshi. Anty Sumayya ce tace. "Na tausaya mata matuƙa. Uwar mijinta na farko bata da imani. Na jinjinama aurenta na biyu da irin yadda soyayya ta jata. Ta kuma yi kuskure da a saninta ta auri Hamma alhalin tasan wacece Hama. Amman ƙaddarallah. Yanzu Hajiya uwani tunda Hajiya Iyabo bata da ishasshiyar lafiya ki bamu lambar Hamma, da lambar Debisi mu kirasu sai su zo su samemu. Akwai wani alƙali dake alƙalanci a kotun musulunci zamu gayyaceshi yazo ya warware mana wannan ƙullin. Usman kayi haƙuri dan Allah ka daɗa nasan kayi. Ita ƙaddara ta rigayi fata. Ka duba da duk irin soyayyar da Iyabo tayi ma Hamma ko zaman shekara ɗaya cib basui ba. Kai kuwa sai da ka shekara goma sha bakwai da'ita ta haifa maka yara har uku duk kuruciyarta kai ka kwashe ta. Nasan irin son da kake yima Iyabo da irin tasirinta a rayuwarka ka dangana ka karɓi duk abinda Shari'a tazo dashi" Uwani ta ɗaga waya ta kira Hamma. "Hajiya Uwani barka da safiya ya Kano da yaran? "Malam Hamma kowa yana lafiya. Dama na kiraka ne muyi magana da kai. Gani a Gombe kuma cikin amincewar Allah mun haɗu da Iyabo yanzu haka muna tare a gida ɗaya tare da yaranka ma. Kazo ka sameni a Gombe dan Allah in da hali kazo da wani babba domin akwai wani babban ƙulli" "Allahu Akbar. Allahu Akbar Allahu Akbar ya Allah nagode maka Allah na gode maka ashe zan sake ganin iyabo. Mustafa inane gabas zanyi sujudul sukur" Yake tambayar na kusa dashi. Hamma duk ya birkice ya saki kukan murna yanata jero addu'o'in godiya ga Allah. "Uwani nagode gobe zamu tawo yanzu zan kama hanyar Adamawa" Nan Uwani tana share hawaye ta zare wayar a kunnenta ta kira Debisi nan shima suka ruɗe da murna duk aka tsaya akan gobe suma zasu tawo. Usman yayi shiru sai Allah yake ambato a zuchiyarshi kawai. Yaranne suka zo suka fice daga gidan. Dr kuma ta shigo sake duba jikin Iyabo. Uwani ta miƙe tabi bayan Dr, Alhaji Usman da Anty Sumayya suka fita Nan duk wanda ya dace su zauna dasu dangin iyayensu manya sun zauna sun tattauna an fasa matsalar dai. Cikin ƙanƙanin lokaci aka san halin da ake ciki. Ga Usman a zaune Suna karbar gaisuwar makoki amman hankalinshi baya tare dashi. Ƴan biyu dake zaune a jere dashi kawai yake ji a halin yanzu Iyabo kam ya riga da yasan ta kuɓuce mishi in ba wani ikon Allahn ba. Amman yana ji a ranshi da iyabo zai ƙare rayuwarshi, irin sonda take nuna mishi yafi son da tayi ma Hamma a baya a labarin da Tabalbalin ta bashi. Idanunshi yake lumshewa lokaci zuwa lokaci. IYABO:. Tare Uwani da Dr suka shigo. Bayan Dr ta gama dubani ta fita Uwani ta soma bama Hajja Mama labarin matsayar da aka tsaida lamarinnan. Ni dai sai cikina ya zuge zawo duk minti biyar sai na faɗa banɗaki. Mijin Uwani da kishiyarta ne suka zo yi mana sallama. A hankali na fita falon na zauna a waje guda muka gaisa cike da girmamawa a mutunce. Su kai mun barka da dawowata cikin hayyacina tare da adda'ar Allah ya kare gaba. "To mu Hajiya jirginmu zai ɗaga ke sai yaushe kenan zamu saka rai dake?" Uwani tayi dariya tace. "Ranka shi daɗe ni nan ai sai naga abinda ya ture ma buzu naɗi, zan zauna da'ita har zuwa a gama komai in sha Allah sai in dawo" "To ai Shikenan. Amman yaran shago sun kiraki kuwa, ruwa ya shigar miki shago yayi ɓarna sosai gaskiya. Amman nace su kai kayan da ruwa ya taɓa gida a wanke a shanya dai. Na kuma tura musu masu gyara su gyara inda ruwan ya shiga" "Assha to Allah yasa da abinda ya tare. Basu ko kirani ba gaskiya" Ni dai nan nayi musu Allah ya tsare hanya na sa kai na koma ciki. "Iyabo bari in shiga cikin gidan mu gaggaisa tukunna. Wai ni kam kishiyoyinki me suka ɗauki duniya ne sunfa fito lokacin da kika faɗi a can tsakar gidan fa. Amman banga sun zo dubaki ba, su Sumayya mun musu uziri su mutuwa akayi musu." Ohon musu Hajja ai babu komai duniyarma nawa take. Wallahi Allah gabaki ɗaya komai na cikin duniyarnan ya isheni ya isheni. Kafin Hajja Mama ta bani amsa Anty Sumayya ta shigo da sallama tare da cewa. "Imanine yadda da ƙaddara me kyau ko akasin hakan Iyabo. Na sani al'amarinnan babbane sosai, amman ki godema Allah daya dawo dake cikin nutsuwarki zaki ga danginki, ki ga mahaifanki me yafi wannan daɗi ko babu komai yaranki zasu ga mahaifinsu. Ki sani dan suna amfani da sunan Usman duk daren daɗewa za'a samu ko a family da wasu zasu tsokata musu cewar Usman ba mahaifinsu bane. Ko ba'a tsokata musu ba ranar da Usman ya faɗi ya mutu a ranar zasu yi kuka dan dole a fayyace musu gaskiya da gaskiya. Hakan ma ban yi tunanin zai kai tsawon haka ba, nayi imani da a Gombe kuka zauna tare da kishiyoyinki ko su Abida zasu goranta ma yarannan. In ma ba sui ba iyayensu zasu yi. Kinga sai ki shiga tashin hankali dan ko yankaki za'ayi ba zaki ce ga ubansu ba, mu kuma zuchiyarmu a lokacin zata shiga wasi_wasin shi yarsn ma na sunnah ne. Ke komai kika ga ya faru akwai hikma a tattare da faruwar. Ki yi haquri daga ke har Usman din. Shima yana cikin mummunan halin da tunda nake ban taɓa ganinshi a ciki ba." Nasiha da ban baki kawai ake ta yi mun. Sai nayi kamar na samu nutsuwa dana ga shige da ficen yara sai damuwa ta sake aurena. Sai zuwa yamma akaita cincirindon zuwa gaisheni tare da gulmace gulmace a madadin su tausaya mana sai abun ya zama wani iri kuma. Suhailat kuwa sai cemun tayi. "Ashe komai yazo ƙarshe kuma, hankalinki ya dawo jikinki an gano kina da aure. Ƙila ma kina sane dokiya kika zo ci, to dubu ta cika". Uwani ta dubeta tace. "E yadda kika faɗa haka ɗinne baiwar Allah. Sai dai mu gode ma Allah daya nuna mana wannan lokaci kuma. Dukiya kuma ai tari da ta handami iyakar handamarta karfa ki mance Iyabo itace da miji, ko ya baku labarin adadin gidajen da ya sai mata ita da yaranta kuwa?"" Bata dai kula Uwani ba ta fice. A zafafe dan maganar Uwani ta daketa sosai. Duk da bata san Usman akan rashin adalci ba, akan Iyabo sai take ganin zai iya komai ma akace yayi. Yaranshi basu sami damar karatu a waje ba sai ƴaƴan Iyabo harda agololi. Uwani har yanzu kina nan da halinki" "Me kike ganin za'a fasa Iyabo. Ya zata zo tana faɗa mana magana. Ke dai kullum a haka zaki ƙare ƴar iska. Dole Uwani sai da tasa na dara. Wannan daren cike na kwana da zulumi gami da taraddadi har garin Allah ya waye. Sukuku nak, gabana kuwa dama shi tunda na dawo hayyacina yake faɗuwa. Ƙarfe biyun rana su Debisi suka iso. Amman Alhaji Usman ya ajjiyesu a can cikin gida ana jiran isowar su Hamma. Su kam sai dab magriba Allah yayi musu karasowa bayan an idar da sallah Alhaji Usman ya shigo da sallama. Ina ganinshi na saki kuka. "Uwani Hajja Mama kuje falo baƙinmu sun hallara. Inaso zan gana da Iyabo" Nan suka fice suka bamu waje. Zama yayi a kusa dani yayi shiru sai ajjiyar zuchiya yake yi. Cikin wata murya mai kauri yace. "Wannan ƙaddarar da girma take. Allah ya bamu dangana baki ɗayanmu Iyabo. Amman me yasa kika boye mun halin da kika samu kanki kuka haɗa baki da Hajja Mama tace ke ƴar ƙanwartace ashe a gari ta tsintoki?" Muuryata da bakina yana rawa na bashi labarin yadda mu ka yi da Hajja Mama. Sonka ne ya rufe mun idanuna shi yasa har na amince dan gudun a faɗa maka gaskiya ka fasa aurena. Wallahi babu wani nufi mara kyau a tattare dani ka yarda dani wallahi Usman ina sonka so mai tsanani" Murmushi yayi mun idanunshi cike da hawaye yace. "Ni ko nasan kina sona,amman ai dawowarki hayyacinki tuni ya ture gwamnatina dan Uwani ta bani labarin soyayyarki da Hamma. Ashe kyakkyawane haka shi yasa ƴan biyu suka fito kamar larabawa." Usman... Na ja sunan nashi yayi maza ya runtse idanunshi. "A_a Iyabo kar ki mun wata kalmar soyayya. Ina neman alfarmarki dan Allah in aurena dake ya ƙare kiji tsoron Allah ki cire ni cak a zuchiyarki kar ki sake ki zauna kiyi tunanina. Sannan zan sake roƙon wata alfarma duk da ba lallai bane in samu ba kuma baki da ikon yanke hukunci ke kaɗai Iyabo in na rasaki na rasa su Hassan zan shiga damuwa mai tarin yawa. Duk da a tunanina ke kike da zaɓi a kanmu ko ni ko Hamma. Nayi imanin in dai hakanne dole ni zaki ɗauka ba Hamma ba, ki rayu tare damu iyabona cinyar sa maganin mai haɗama ki zaɓeni kar ki ga Hamma ki juya mun baya. Zaki mun illa. Inason su Hassan ina son su wallahi... Na baka su har abada Usman babu wanda ya isa rabaka dasu. Yanzu Usman aurenmu rabawa za'ayi kenan? In dai zabi aka bani na shiga ukuna ya zanyi da rayuwata wa zan ɗauka wa zan ajjiye to" Na fashe da kuka. Mun daɗe a haka sosai har sai da Uwani ta shigo ganin halin da muke ciki sai hankalinta ya tashi. "Kuyi haƙuri dan Allah. Usman ku fito muje" Ficewa yayi fuu. Uwani tazo ta ɗagani muka fito falon Tsarki ya tabbata ga Allah mai kowa mai komai Da Yaya Hamma na soma haɗa idanu, na ganshi ya goge sosai ya zama ɗan birni sai dai ramarshi data ƙaru da ɗan duhu da yayi. Ga Baɗɗo, ga Amaduyal, ga Yafendo A'i. Ta ɓangarensu Burodami Debisi kuwa. anty Ramata, Burodami Kokodeen, Burodami Debisi, da Iyaa Beji ne suka tawo. In taka in isa gabansu ni dai na kasa. Hamma ne kaɗai ya miƙe ya iso gareni ya tsaya a gabana. Usman ya hadiye yawu tare da yin gyaran murya. Baɗɗo ce ta ƙaraso muka rungume junanmu sai kuka, ɗakin ya cika da koke koken mata a haka su Hassan Anty Sumayya ta shigo dasu. Nan kallo ya koma garesu tsugunnawa Hamma yayi yasa goshinshi a ƙasa yayi sujjadar godiya ga Allah daya nuna mishi wannan rana. Zan barku anan kuka yaci ƙarfina A tunanin ku auren waye dahir a kan Iyabo ne? Shin zaɓin za'a bata kamar yadda Usman yake fara da buri? To wa Iyabo zata zaɓa a tsakanin Usman da Hamma. Yaranta uku da Usman, yaranta biyu da Hamma. Usman yayi mata so zallah, ya inganta rayuwarta da rayuwar yaranta, tayi rayuwar farin ciki tare dashi. Hamma ya sota a baya ya sai da shanu har biyu domin farin cikin Iyabo, wanda a wajen bafullace babu abinda ya kai shanu daraja, kuma shekara sha bakwai yana zaune yaƙi aure sabida Alaja Iyabo, bugu da ƙari gashi ɗan uwanta na jini. Shin wa zata ɗauka wa zata bari? MRS BUKHARI **Anty Ramlex Me kayan Da'a,ingantattu,fitattu,kuma shahararru* Na zo muku da albishir na Promo Promo Promo💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽 Abun da kuka Dade Kuna nema....,hakika dogon Jira ya kare.....Ga abunda kuke bege gaba gare ku💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽ba sai kunyi godiya ba menene amfanin zaman tare😌🤫😉 Ina Uwargida me son sabunta martabarta a wurin Oga,Ina amaren bana masu son su mallaki zuciyar ango,Ina zawarawa da suka shirya gyaran abun cikin buje,domin farfado da mutuntakarsu........ku matso kusa...... Hajiya ta sauke farashi,me kike jira........ Babban set na promo ~#20k~#15k👌🏼 🎯 _dambun zabuwa 🎯tsumin bugenta shakaf 🎯Gumbar Madara me Sanya megida Santi da dalalar yawu 🎯Hadin dabino da cukwui hadin basarakiya 🎯Tsugunno me sirri_ *Karamin set*~#15k~#10k💃🏽 📯Herbal for vaginal infection 📯Tsimin bujenta shakaf 📯Gumbar Madara da hadin dabino. 📯Hadin dabino da cukwui (manta uwa) 📯Tsugunno me sirri 🚚Muna aika kaya ko Ina a fadin Nigeria da kewaye. 📞Ku tuntubeni a wnn numbern 07069722234 Anty Ramlex taku ce🥰 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU 19 DA SADAUKAR DA WANNAN SHAFIN GAREKA MIJINA ABIN ALFAHARI MASOYI MAI KAMA DA ZUMA. BUKHARI IBRAHIM LADAN. "Am ina ganin kuka duk ba naku bane face ku nuna godiyarku ga Allah. Ku zo ku zazzauna muyi abinda ya taramu a sallami kowa. Cewar Anty Sumayya kenan. Hannuna Baɗɗo ta kama ta zaunar dani a ƙasa gefen ƙafar Yafendo A'i kaina a ƙasa falon ya ɗauki shiru. Alhaji Usman ne yayi gyaran murya ya soma jawabi a hankali kuma a sanyaye tun daga haɗuwarmu har zuwa yau ɗinnan. Yana gamawa falon ya ɗauki salati da tafa hannaye. Idanuna na ɗago na dubi Yaya Hamma idanunshi sun koma jawur farin cikinshi ya koma baƙin ciki jikinshi har rawa yake yi ƙirjinshi yana ta hawa da sauka, hawayene naga suna bin kumatunshi kawai, kunsan fa Yaya Hamma akwaishi da kishi. Idanuna na lumshe kawai wasu hawaye masu zafi suka zubo mun. Alhaji Usman yace. "Hassan Husaini wannan shine mahaifinku, waɗannan dangin mahaifiyarku ne. Kuje ga mahaifinku yasa muku albarka" A sanyaye yaran suka isa ga Hamma yayi musu wata iriyar runguma kukan kishin da yake dannewa ya saki kawai. Niko tsabar hawaye ko gani bana yi ma. Yaran sun daɗe sosai a jikin Hamma kafin alƙali yace yaran su ɗanje daga waje tukunna, a samu a yi abinda ya dace. Alƙali yace. "Wanan shine mijin ita wannan baiwar Allah?" Yaya Hamma ya ɗago kanshi yace. "E nine ranka shi daɗe" "Ko zamu iya jin labari daga naku ɓangaren dangane da ɓatan ita Iyabo?" Uwani ce tayi gyaran murya ta basu labarin komai. Falonnan ya ɗauki shiru, can alƙalin yace. "Tsawon tafiyarka shin Iyabo ita ke ciyar da kanta, ko kuma kai kake ciyar da'ita, duba da yadda ka daɗe a wajen kiwo, duk da wannan daɗaɗɗiyar al'adace da akasan fulani da'ita tun zamanin baya." "Ranka shi daɗe mahaifiyata na kula dasu, sannan ƙannena maza na kulawa dasu su suke ajjiye hatsi, ɗan kuɗin cefanene suke nema da kansu" "To Alhamdulillah naji bayaninka Alhaji Usman, suma ɓangaren Hamma naji nasu bayanin. Da kai da Iyabo, da Hajja Mama baku da laifi ko kaɗan ita Iyabo hankalinta aka gusar mata rayuwarta ta baya ta mance. Ita Hajja Mama bata san bayan Iyabo ba, kai baka san tana da aure ba wannan abun an yishi ne a bisa rashin sani, baku da laifi har a wajen Allah. Ina fata bayan bayyanar wannan lamarin babu wata mu'amular auratayya data shiga tsakanin ku?" Alhaji Usman ya ja ajjiyar zuchiya ya sauke kana yace. "Babu ranka shi daɗe" "To Alhamdulillah. A zahirin gaskiya dawowar iyabo hayyacinta shi yake nufin aurenku babu shi ya ƙare ya zama tarihi, har gobe tana a matsayin matar Hamma tunda yana da ranshi gashi a gabanmu, babu makawa aurenku da kanshi ya warware kanshi ba'a buƙatar sai ka rubuta takadda. Sai dai ku ɗauki dangana kawai. Ƴaƴa da kuka haifa yarane na sunnah tunda ta hanyar aure aka samesu kuma suna da gado kamar sauran yara. Tare dukkanmu ukun muka ɗago muna kallon alƙali illahirin jikina rawa yake yi, Alhaji Usman yace. "Allah shi gafarta ina bayani akan za'a iya bata zaɓi ta zaɓi da wanda zata yi rayuwa? Naji kace aurena dake kanta ya mutu" A raunace yayi maganar, alƙali ya gyara zamanshi yace. "Ba irin wannan case ɗin bane yake ɗauke da irin wannan hukuncin ba Alhaji Usman. Ita wannan baiwar Allah hankalinta ne ya gushe ta baro bayanta, ta manta komanta, kai kuma ka aureta, sabida haka bata da zaɓi dole aurenta na farko yananan daram. Shi wancan da kake maganar zaɓi shine in shi mijinne ya tafi ya barta shekara da shekaru babu waiwaye babu aike, babu ciyarwa har an cire rai da dawowarshi to sai taje kotu alƙali ya saketa tayi wani auren, to bayan tayi wani auren in shi wannan mijin ya dawo shine alƙali zai bata zaɓin zaɓar ɗaya a cikin mazajen nata. Kaga kuwa ai naku case ɗin ba haka bane, da fatan kun gamsu?" Idanuna na runtse ina ambaton Allah. Alhaji Usman ma inaji yana ambaton Allah a fili, ya kasa mallakar kanshi" "Yanzu abu na ƙarshe shine Iyabo zata yi idda na wata uku, ko kuma ince jini uku dan wata mace a wata biyu take yin jini ukunta. In kuma ta wuce yin jinin al'ada sai ta ƙirga wata uku. Da zaran wannan lokaci ya cika Iyabo zata koma ɗakin Hamma a matsayin Matarshi suci gaba da zama, ba sake ɗaurin aure, ba sabon sadaki, ba akwati. Wannan shine hukuncin. Da fatan zaku bi yadda yazo a musulunci kar abi son zuchiya duk da akwai malaman da suke ba da fatawar macen na da damar zaɓan da wanda zata zauna a hakanma. Zance mafi inganci shine dole ta koma hannun mijinta na farko.wannan shine ƙarshen maganata." A hankali sautin kukana ya dinga shiga kunnuwan jama'ar cikin falon hankalina ya tashi sosai da sosai. Bayan an barni nayi kuka ishasshe sai Usman yace. "Ina neman alfarma ɗaya a wajen Iyabo da Hamma. Hassan da Hussaini sun riga sun zame mun jinin jikina so nake a barsu a hannuna ko baku barmin su halak malak ba a barsu su ƙarƙare digree da mastas ɗinsu dan Allah ni wannan alfarmar nake nema musu a dubeni. Nasan Hamma shima zai so a yanzu ya tattare kan iyalinshi waje guda, ku dubeni kuimun adalci dukan zai yi mun yawa zai yi mun yawa Hamma" Anty Sumayya sai ta fashe da kuka. "Nima damuwata yaranne wallahi Allah, mun yi shaƙuwa dasu sosai ya zamu yi Hamma ka tausaya" Gyaran murya Hamma yayi nayi saurin ɗagowa na dubeshi, ashe Usman yana ankare dani, ina sake ɗagawa muka haɗa idanu Ba shiri nayi ƙasa da kan nawa. "Alhaji Usman zan soma maka da godiya. Wallahi Allah da ace ina da ikon bar maka Iyabo da na bar maka ita. Balle su Hassan, haƙiƙa ka fini son su, ka fini shaƙuwa dasu, sabida haka na barsu a hannunka su yi zamansu tare da ku. Sai dai in da hali kuma ku bamu daya a cikin yaran ita iyabon gudun kar kaɗaici yayi mata yawa. Mun gode ƙwarai Ubangiji Allah ya saka maka da mafificin alkhairi wannan hidima da kayi da iyalina har gaba da abada bazan mance ba. Malam kaima mun gode sosai da kasancewarka tare damu Allah ya saka da Alkhairi " Wawuyar ajjiyar zuchiya na sauke da naji Alhaji Usman yace. "Ta ɗauki Rumaisa'u autarta tunda nayi muku bayanin mun juya mahaifarta sakamakon ciwon bayan data kwaso a saudiyya sai kai mun afuwa bansan cewar haka bane abun da duk abinda ya faru bazai faru ba. Inma su matan take so harda Nana ta ɗauka wallahi bazan hanata ba, sai dai da sun kammala sakandare zasu zo su sameni a India zasu jona digree ɗinsu suma likitocin nake so su zama. Nagode sosai Iyabo da irin zaman da kika yi damu Allah yayi miki albarka. Kai kuma kaji tsoron Allah ka dubi Iyabo kai mata riƙon da zata yi alfahari da dawowarta cikin hayyacinta" Akwai motarki a harabar gidannan in zaku tafi to ki tafi da abunki. Wannan gidan da kike ciki na mallaka miki. Sannan ga wannan babu dai yawa million biyar ce ko sana'a sai kiyi dasu. Yaran zansa a shiryasu ku tafi Anty Sumayya zata biku taga wajen." Yana gama fadar haka ya zaro takaddun gidan yasa hannu, nima nasa, Burodami Debisi da uwani suma suka saka, sai alƙali ma ya saka. Ya rubuta mun check ya bani. Usman ya saka kai ya fice a falon ko waige bai ba. Ji nayi kamar in bishi, dan har na so tashi kaifin idanun Hamma ne yasa dole na zauna kaina a ƙasa ina kukan zuchi. Ƴan uwa anata murna falo ya gauraye da jin dadi da farin ciki, sai waye waye suke yi. A wannan zama ne naji abun alkhairi da uwani ƙawa ta gari ta yi mini dukiya ta habaƙa ta girma. Yau ni Iyabo na zama nurse gani da gidaje, gwala-gwalai, ga mota, ga Hamma ya dawo mun, ga Dadana tana da rai gani cikin dangi tsamo_tsamo amman wallahi Allah bani da nutsuwa kunji fa wata ƙaddara tausayin Usman ya hanani samun lafiya da tsantsar son shi. Bazan ɓoye muku ba inason Usman so mai yawa, shekara goma sha bakwai bafa wasa bane. Kuma a wannan shekarun rayuwarmu muka gudanar cikin aminci, wayewa, da sanin darajar juna madallah da salihi kuma nutsattse Usman. A wannan rana bamu samu ganawa da Yaya Hamma ba, ina dai cikin ƴan uwa anata bani labarin rashe_rashe da ƙaruwar da aka sassamu. Iyaa Debisi ta rasu shekara uku kenan ashe babu rabon zama gana. Iyaa Kokodeen kuma tana raye babu dai yadda take, su Bose da su Burodami Debisi sun manyanta sosai ga iyali sun tara masha Allah. Yaya Hamma ya samu ganawa da yaranshi sai farin ciki yake yi. Yaran dai basa wani farin ciki duk sun shiga damuwar zan tafi in barsu su kaɗai. Ni dai haƙuri na basu na zaunar da yaran duka naita musu nasiha, su manyan nai musu bayanin da zasu iya fahimta dai. Suka shiga dangina suka sake. Washegari muka ɗau azamar tafiya Kano kafin mu wuce Jaɓɓi lamba. Ni a motata muka zauna Burodami Debisi ne zai tuƙa. Da yaran dukka muka tafi Anty Sumayya zata dawo da Alhaji karami. "To Iyabo Allah ya ƙaddara saduwarmu ku gaishe da ragowar dangi, nima zanzo in sha Allah" Cewar Alhaji Usman. In yi magana na kasa wallahi, in yi sallama da matanshi da matan ƙannenshi ni dai na kasa haka muka kama hanya. Gaga_gaga sai gamu a kano can gida. Naga soyayya muraratan ƴan uwa da maƙota duk sun taru. Wata ƙudurar Allah a nan muka haɗu da Gwadabe da su Toye suma sun zo harda Bara'u a shirgegiyar motarsu Gwadabe ya haɗa ƙiba da katon ciki, girma ya saukar mishi sosai. Yara sun girma masha Allah Allah al hakeem yau Gwadabe ne zaune a cakuɗe da ƴan gidanmu a ɗakin iyaa Debisi rayuwa kenan komai mai wucewa ne. Nan ma Gwadabe suka tafi suka bar mun yara. Suna fita ƙofar gida Gwadabe ya dubi Bara'u yace. "Hmm Iyabo ce yau ta zama nurse harda rayuwar aure a India. Bara'u na taya iyabo murnar dawowarta hayyacinta ta wani ɓangaren na taya ta takaicin baro india da tayi. Nifa Hamman nan nata Allah cikin amincewarshi naƙi jininshi" Bara'u ya dafa Gwadabe yace. "Kamar yadda har abada Hadiza ba zata ƙaunaci Iyabo ba. Allah ya shiryeka shaƙiyi" Kwananmu biyu a Kano muka yi Adamawa gabaki ɗayanmu. Allah mai iko Dada ta tsufa ta yamushe, amman da kafarta take tafiya muryarta raɗau. Kuka kawai ta dinga yi na murna. Dangi akaita tururuwar zuwa kallona, maƙota ɗalibaina, Chubu dake aure a birni, Daso ne da duk ta lalace ta tsofe duk kowa yazo baƙi sun ƙi ƙarewa sun ƙi barinmu mu keɓe. Kwanan Anty Sumayya da Hajja Mama biyu a jaɓɓi lamba suka tafi tare. Alhaji Ƙarami yanata kukan shi zai zauna da Nana. Haka dai sukai mana sallama suka tafi ƴan biyu kuma mun roƙi ba yanzu zasu koma ba tunda lokacin ne ma ake zuwa yi mana barka. Ɗakina nasa Baɗɗo ta kaini na shiga komai yananan daram a ɗakin babu ko datti. Saboda a nan Hamma yake sauka in ya shigo Jaɓɓi lamba. Tsugunnawa nayi naci kuka iyakar iyawata. "Uwani kin tuno sanda aka kawonu ina Amarya idonmu idon azara?" Dariya muka tuntsure dashi. Uwani tace "Ni danna kan hama a ruwan wanke_wanke shi yafi komai tsaiwa a raina ƙawata. Baɗɗo tace. "Hmmm ai Hama ko a haka ta ga aya. Dan har yanzu batai aure ba tana gidan yarta sai tallar nono rayuwarta abun tausayi. Ajjiyar zuchiya na sauke. Nasan dayawa a cikin makaranta burinsu ganin Hama ƙila ta haukace ko ace tayi haɗari tayi raga raga ko? Kamar yadda yake faruwa a ƙagaggun labarai, ko ace muna haɗa idanu ta fita a guje tana hauka ko? Wannan ba haka bane labarine na gaskiya wata shariar sai a lahira, wani sakamakon sai an je gaban mai kowa zai cire maka hakkinka, ni ko a iya kasa auruwa da tayi raina yayi fari abadan babu yafiya a tsakaninmu, ni bamma sake sakata a idanuna ba. Amman naji labarin wulaƙantacciyar rayuwar da take yi a gidan yarda da irin yadda aka washeta a ƙauyen ta zama tamkar mujiya. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI NAMA YA DAHU.... ROMO ƊAÑYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI LITTAFI NA HUƊU 20 ƘARSHE NA SADAUKAR DA WANNAN SHAFIN GA DUK ƊAUKACIN MASOYANA IYABO Gaga_gaga Rayuwa taci gaba da shurawa, ina zaune gani ga Dadana ina idda, ganina tare da,ita ya sata farin ciki mai girma. Bayan kwana hudu da zuwanmu Uwani ta shirya ta ta koma gida. Tafiyar Uwani da sati biyu Alhaji Usman ya turo aka zo aka tafi da su Hassan, ina hawaye na rabu da yaran bayan nayi musu nasiha mai ratsa jiki, kuma na koresu da su dinga kiran Hamma a waya suna gaisheshi kamar yadda zasu kirani. Gwadabe ma ya turo aka ɗaukar mishi yara Bara'u. Hamma kuma ya tafi Sokoto yana ta shirya gida dan tarewata, ni kuma ta nawa ɓangaren inata rarrashin Dada ta bini muje. Amman wallahi tsohuwarnan tace in barta ta mutu a mahaifarta zaifi mata. Su Yafendo ma suka ce bazan ɗauketa ba dole haka na haƙura, sai dai na zage na kashe kuɗi na zuba mata kayan alatu, na jibge mata kayan abinci masu yawan gaske. Ana saura sati biyu in fita idda na tambayi Yaya Hamma inaso zan shiga Kano zan yi siyayya. A lokacin ya dawo jaɓɓi lamba yayi sati biyu ya sake komawa Sokoto. Ranar lahadi Uwani na zaune a falonta sai taji sallamata ni da ummi ƙanwarta. Da su Nana "Iyabo kece da daddare haka da yarana? Allah sarki ashe wannan lokacin zai dawo Iyabo lokacin da zaki ci gaba da ziyartata?" Uwani ta balbalin duniya. Lallai kin samu duniya sosai irin wannan daula da kika miƙe ƙafarki a ciki haka?" Hannu ta ban muka tafa. Kafin na nemi waje na zauna. Kin ganni na shigo siyayya saura sati biyu in fita idda. Uwani amma ina cikin matsala damuwa tayi mun yawa shi kanshi Hamma ya rasa gane kaina. Dan ko jiya sai da ya tambayeni anya kuwa har yanzu ina sonshi. Soyayya ɗaya ce kuma Hamma nake yima. Amman tausayin Alhaji Usman yayi yawa a zuchiyata. Uwani bawan Allahnnan ya nuna mun ƙauna ya kula dani kamar ƙwai. Wannan kyautatawar tashi itace take hanani sakewa da Yaya Hamma kuma abun sai in dinga ganinshi wani iri. ( Ba kowa ne zai gane halin da nake ciki ba, sai wanda makamancin haka ta taɓa faruwa dashi, ko kuma wani nashi) Hawayene suka zubo mun. Uwani tace. "Allah ya kyauta Iyabo. Amma ki sani ya zame miki dole ki dena wannan kuka hakanan da wannan damuwar dan bata da rana. Sannan kuma abune mai wuya ki iya goge rayuwarki a gidan Usman a zuchiyarki ki yawaita ambaton Allah ki yawaita yi mishi adda'a sai kiga kin samu salama. Yau zamu kwana muna hira kenan hirar yaushe gamo tunda yanzu mun nutsa" Bayan mun yi sallah munci abinci ummi har ta tafi muna kwance a gado. Uwani na bani labari nima ina bata labari. Labari har ya zagayo take tsokatamun ai gwadabe gashi_gashi ya riƙe kujera, yanzu haka suna kasuwancin magani shi da Bara'u. Wannan labarinne yasa ni kuwa nace gobe mu shirya muje Takai ɗin in je in dubo yara, in ga matan Gwadabe kuma" Washegari na ɗauki ado na ɗauko sutura mai tsada na saka ga gwal ga komai. Nike tuƙa motar Uwani har Takai. Uwani ta cire waya ta kira Gwadabe ta sanar mishi da zuwanmu. Nan da nan sai gashi ya zo ya taremu. "Iko sai Allah tsuntsun soyayya yau kune a Takai. Allahu Akbar" Cewar Bara'u ba sai naji zanyi kuka ba, da ƙyar na mai da kukan, tuno yadda muke zuwa Takai ni da Gwadabe hajaran majaran, da irin wulaƙancin dana fuskanta a Takai, sai na saki murmushi dana tuno Babala. GWADABE kuwa ya kasa magana sai kallo. Motar Gwadabe na gaba ina bin bayanshi har cikin gidanshi. Suna tafe muna binsu har cikin babban falon gidan Gwadaben. Ai kuwa yaran duk sunana, wasu na falon wasu basa cikin falon. Su Kayinde suka zuba mun idanu, da suka gane nice sai suka nufo ni a guje suna ambaton umma, umma" Zama mu ka yi, Gwadabe ya shiga ciki kiran matanshi. Ni kuma na shiga ƙarema gidan Gwadabe kallo. Ina mamaki yau gani a gidan Gwadabe a matsayin baƙuwarshi Yarane suka fito su Toye an zama samari sosai Can sai ga Babala ta fito da fara'arta ta nemi waje ta zauna.. "IYABO barka da arziki kune a tafe?" Murmushi nayi na tsugunna har ƙasa na gaishe da Babala cike da girmamawa. A mugun kunyace ta amsa mun gaisuwata tare da yi mun jajen jarabawar data sameni. "Iyabo a yi haƙuri a yafe ni dan kusan duk nice ummul aba'isin faruwar komai. Haƙiƙa na ɗauki darasi naga aya. Na kasa yafe ma kaina gani nake yi nice na jefaki a wannan hali. Allah sarki Babala wallahi babu komai tun da ban riƙeki ba har cikin raina Allah ya yafemu nima in nayi miki laifi ki yafe mun. Ina su Yaya Hambali kuwa?" Na ɗauke zancan.." "Hmmm yana can Kano tare da matarshi, tallan zoɓo ma take ɗaura mishi. Gwadabe ma yayi yayi ya jawo wan nashi jikinshi ya bashi jari wallahi mitsiyaciyar matarshi Layla taƙi. Layla yake aure wacce a baya naso Gwadabe ya aura. Duka take yi mishi ta mayar dashi sauna wallahi, sai in fi wata nawa ban sashi a idanuna ba ma" Ta ƙarashe maganar kamar zata yi kuka. Ajjiyar zuchiya na sauke ina mamaki. Sai ga Gwadabe da matanshi sun fito. "Ah maraba lale Anty Iyabo yau ashe muna da manyan baƙi" Cewar Shafa da fara'arta Hadiza kuwa tayi Magana ta kasa sai kallona kawai take yi ni kuma sai basarwa nake yi. Nan dai aka zauna, sai ga Sakina ina ganinta na miƙe muka rungume juna cike da fara'ar yaushe gamo. Mun gaisa naga yara duk sun girma sunata jami'a dan Gwadabe yace bazai aurar dasu ba sai sun gama karatu sun soma aiki tukunna nayi farin ciki sosai da hakan. Inata mamakin matar Gwadabe dan ko gaisawa bamui ba tana ta haɗe rai. Da za mu tafi nayi ma Shafa da Babala alkhairi na kudi, suma yaran nasu daban, na takwarata kuwa na musamman ne. Bayan mun yi sallar la'asar anci an sha mu kai musu sallama a mutunce. To a Kano nayi gyaran jiki na yi duk abinda ya dace Uwani ta zagaya dani gidajen da duk su ka sai mun. Sai na kira yaya Hamma a waya mu ka shawarta ina son in zauna a Kano in da hali tunda ga gidajenan dani ni Sokoto ba wani daɗi zatai mun ba. Shi kuma ya nuna mun sana'arshi ta samu kafuwa sosai to sai na haƙura na koma Jaɓɓi lamba bayan na ziyarci su Burodami Debisi. Ina isa na samu Hamma yayi mun akwati uku shaƙe da kaya na garari. Su Chubu sai shirin rakiyata suke yi. Ranar dana gama iddata aka tara dangi mota biyu da tawa motar da motar Yaya Hamma akai mana rakiya Zuwa Kano a maimakon Sokoto tunda na sadaƙar yace can yake son mu zauna sabida kasuwancinshi ya kafu. Dada ta riƙe hannuna ta dinga yi mun adda'a tana tofa mun. Idanuna a rufe inata rera kukan da bansan na menene ba. Tafiya yankin azaba. A gidana na titin mandawari na tare madaidaici mai kyau ginin zamani, gashi yasha tsadaddun kaya wanda duk Yaya Hamma ne yayi mun da taimakon Uwani dan ita ashe ya faɗa mata zan tare a Kano ɗin tunda na nuna hakan nake so. Nanma aka gama bikin da za'ayi washegari su Baɗɗo da Chubu suka juya gida ya rage daga ni sai su Nana. Uwani ma ta tafi tace gobe zata sa a kawo mun kayan kari. Da daddare na caɓa ado irin na amare ina zaune a falo sai ga Yaya Hamma ya shigo yana sanye cikin farar shadda dinkin malum_malum ga hular zanna a kanshi yanata ƙamshin turare. Hannunshi shaƙe da ledar kajin amarci. Miƙewa nai da sassarfa na isa gareshi na faɗa ɗan ƙirjinshi yayi mun riƙon alewar yara sai na saki kuka da naji ɗuminshi. Shi kuwa ya shiga aikin rarrashi. Ya riƙeni dam a jikinshi shafani kawai yake yi yana tambayata. "Shin mafarkine wannan ko gaske, Iyabona kece wannan a jikina. Tsarki ya tabbata ga Ubangijin daya dawo mun da hankalin matata. Allah na gode maka. IYABO zan baki farin ciki fiye da irin wanda Alhaji Usman ya baki. Zan rayu dake ke ɗaya tak babu kishiya. Wannan dare shine dare mafi daraja sai da mu kai wanka uku a wannan daren kunsan iyabo bani da wasa ta wannan fage. Hamma yana kwance yana baccinshi ni kuma na tashi na zauna na zuba mishi idanu ina kallon kyakkyawar fuskarshi. Ajjiyar zuchiya na sauke kawai Allah al hakeem kenan Duk wata cuta da Hama tai mun ban yafe ba Allah shi zai saka mun da izinin Allah Ƙarshe Anan iyakar abinda na tsunto muku zai tsaya darasin dake cikin labarin Allah ya bamu ikon amfanuwa da kaɗan daga ciki. Ragowar labarin ku ƙarasheshi a ƙwaƙwalenku Kusakuran dake ciki Allah ya yafe mini. Duk waɗanda suka sai littafinnan ku sani da izinin Allah Allah zai faranta mutu dan da kuɗinku muka saka iyayen marayu dariya kuma sun yi adda'a Nera biyar banci ba kamar yada na shaida muku hidimar marayu akayi. Wanne darasi ke kika koya a wannan tafiyar? Menene babban abinda ya fi burgeki A cikin mazaje uku da Iyabo tayi zaman aure dasu wa yafi sonta a naku tunanin? Sai mun sake haɗuwa a wata sabuwar tafiyar da izinin Allah Tafiyar da babu dana sani a cikinta Alƙalami yafi tokobi Ƴar mutan kanuri nake cewa daku sai anjima. Ina godiya masoyana, ina godiya ga dukkan masoyana na faɗin duniya waɗanda suke bibiyar rubutuna. Jinjina ga NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE ƊAKIN SHARHI" JINJINA GA NAMA YA DAHU ROMO ƊANYE PAID GROUP JINJINA GA HAUSA NOVELS GROUP BATI.COM comments dinku na bani nishaɗi. A group ɗin ɗakin sharhi muna gabatar da programs na mutunci, na zamantakewar aure, tare da ba da shawarwari da izinin Allah. Masu gabatarwa ƙwararrune kuma manyane a shekuru da tunani, da kuma rayuwar gidan aure. Nima ina ɗaya daga cikin shuwagabannin, in kina son ki dinga jin muryata kai tsaye ki kasance dani. Mai son kasancewa damu a link nan ya shigo muna maraba da ku masoyan asali. Nagode da jumurin bibiyata da kukai tayi duk da ciwon ido da ya dinga yi mana kutse. Sai na sake fitowa a wata tafiyar da zaku ji daɗinta fiye da wannan