[8/4, 9:03 PM] +234 803 938 4892: NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM 14 Muna gama ci sai ga Yaya Hamma ya shigo. Yana saye da wani yadi mai ruwan bula ɗinkin ƴar shara, yadinnan duk ya gaji yayi laushi sosai sai laɓewa a jikinshi yake yi. Wandon jikinshi kuma na koren yadi ya saka ya ɗauko hular tashi ka fiye naci irin hular da fulani suke mugun so ɗinnan ƴar madina mai fara da baƙa a jiki, ƙafarshi kuma saye da takalmin roba mai ruwan bula duk ya fashe, sai ƙamshin wani turare mai gafin ƙamshi yake yi, daya isa wajensu Yafendo dake akwai fitilar aci bal_bal na gango kwalli rambaɗe a fararen dara_daran idanunshi har zazzagowa yayi. Bayan ya gaisa dasu Yafendo yayi ma Baba bayanin yazo ya kaimu dandaline, sai ya fita waje ya bamu sarari dan mu kintsa. "Daso maza ku tashi ku shirya abun nema ai yau ya samu ko?" Dariya mu ka yi mata kawai. Ni dai mayafi kawai na ɗauka, saye nake da koɗaɗɗen riga da zane. Saɓanin Daso da sai da ta shafa kwalli harda janbakin majigi tasa ma labɓanta. Cikin zaulaya nace. Harda kwalliya ko za'a samo mana bazawari ko?" Dariya tayi kawai tace. "Kayya, ai tunda na rasa Chubaɗo ban sake tsaiwa da kowa ba. Ni abunma wani iri ba fasali yake yi mini" E dole zaki ji banbarakwai wai namiji da suna Hajara. Amman ya muka iya haka Allah ya zaɓar mana. Fatan shine Allah ya sadamu da mazajen da zasu ji tausayin rauninmu. Gara ma ke Daso mijinki rasuwa yayi fa. Ni fa Gwadabe yana doron duniyarnan rabamu akayi a bisa tursasawar mahaifiya da danginshi" Siraran hawayene ban aune ba suka biyo kan kuncina. Dafa kafaɗata Daso tayi jikinta a mace tace. "Mu yi haƙuri kawai mu rungumi ƙaddararmu. Allah yana sane damu, bai mance mu ba. Ta yiwu ya shirya mana kyakkyawar rayuwa a gaba. Ta yiwu kuma wahalar rayuwarmu ne zai fara. Amman duk abinda ya samu bawa ya fauwala shi ga Allah " Wannan gaskiya ne. Muna fatan kyakkyawar rayuwar a gaba. Allah ya sadamu da mazajen da dan so zasu ji kamar su mallaka mana numfashinsu dan mu daɗe mu yi ƙarko. Mu je mun bar Yaya Hamma a waje yana ta faman jira" Kafinma in rufe baki muka jiyo Yafendo tana kwaɗa kiran sunanmu tana yaren Fullanci. Ba shiri muka fito tare da ficewa a gidan. Ko da muka kama hanya, sai cin karo muke yi da mata da samari suna nufar dandali. Ina gefen hannun daman Yaya Hamma, Daso na gefen hagunshi mun sanya shi a tsakiya. Sai hira yake janmu dashi, Daso ce ke bashi amsar duk abinda ya tambaya. Ni tunanin Gwadabe da yarana, da kuma tunanin ta wacce hanya zanbi dan ganin na sanya Dada a farin ciki dariya da walwalarta ta dawo kawai nake. Wani shashe na zuchiyata sai kawai katsaham yace. "Me zai hana ki nemi Uwani in dai bata tafi ba, kema tayi miki hanya ki tafi. In kika tara kuɗi ne kawai zaki iya ɗauke mahaifiyarki ki rabata da azzalumin mijinta, ki kuma rabata da tallan Nono. Wannan shine hanya mafi sauƙi. Tunda ba kya kashe mata aure ba tare da kin shirya mata gidan da zata rayu da yaranta ba, kuma ba zaki hanata tallan nono ba har sai ke kin samu abun yi, ko kuɗi a hannunki da zaki ma rayuwarta hidima kamar yadda mahaifinki yayi mata kafin ya rasu" Nan take sai nake ganin kamar ma na samu mafitar cire Dada cikin ƙangin rashin ƴancin da take ciki. Dan a shirye nake ko matakin shari'a ne zan bi muddin yaƙi sauwaƙe mata igiyar ƙaddararran autenshi. Lokacin dana kwanta jinya take yawan sintirin zuwa dubani. Cubu ranar ta shigo da kuka take labarta ma Yafendo cewar Dada tana gida Baffansu ya daketa ya kumbura mata fuska, sabida sintirin zuwa dubani da take yi wai ya isheshi sai kace nice kaɗai ƴar data haifa. Lamarin da yasa ƙannena suka haɗe kansu suna kuka, tare da adda'ar Allah ya kawo ma Dada mafita ya cireta a wannan ƙangin. Daga ranar kullum ƙwaƙwalwata cikin tunanin sama ma Dada mafita nake, ko da kuwa zan rasa tawa mafitar. Sai yau Allah yayi na tuna abinda nake ganin zai iya kawo ƙarshen hawayen Dada. Tafiya Kano ya kamani gobe da izinin Allah, dan bahaushe gwanin iya tsara zance cikin hikima da azanci yakance da zafi zafi ake dukan ƙarfe, ko kuma yace da safe ake kamun fara" "Jabu tunanin me kikeyi haka mai zurfi har mun iso dandali baki sani ba? Na lura jefa ƙafafuwanki kawai kike yi" Cewar Daso wacce ta kafeni da idanu, Yaya Hamma shima ido ya zubamun, suna sauraren abinda bakina zai furta da sunan amsa. Iska na jawo daga huhuna na furzar kana nace. Tunanin rayuwa kawai nake yi Daso. Ai baka isa ka raba zuchiya da tunani, ko da ayyane_ayyane ba" Na ja bakina na tsuke. Na kura maa wutar karar dake ci bal_bal a tsakiyan dandalin ido, wajen yayi haske sosai ina iya hango kwalliyar mata da maza. Wutar nake kallo yanda take tartsatsi. Amman abinda zuchiyata take ciki yafi ƙarfin tartsatsin wutarnan, jin zafi nake yi daya wuce doka da oda. Hannuna Daso ta kama muka nemi wani benci da babu kowa muka zazzauna. Ƴan berorin ƴan mata sai wasannin gaɗa da waƙe_waƙen su na fulani suke yi. Samari sun kewayesu sai tafi da ɗaga sandunansu suke yi. "Kinga dandalinmu ko Jabu?, Allah yasa wasannin al'adunmu sun burgeki?" Cewar Yaya Hamma wanda yake zaune kusa dani. Murmushi kawai nayi mishi na sauke kayina ƙasa ina kallon yatsun ƙafata. "Jabu tunanin menene ya bujuro miki duk ya sauya kamanninki? Kinga lafiya abun tattalawace ga duk wani rayayye. Me zai hana ki tausaya mana ki dena wannan tunanin ko dan lafiyarki da farin cikin masu son ganinki cikin ƙoshin lafiya?" Kallonshi nayi na mai murmushi idanuna cike da ruwan hawaye. Shima murmushin ya bini dashi, kafin ince wani abun sai ga wani matashi ya ƙaraso gabanmu da sandarshi rataye bisa kafaɗunshi. "Hamma in babu damuwa inaso ka bani dama mu zanta da Daso. Na jima ina bibiyarta domin ta bani damar ko sauraren abunda ke tafe dani taji amman ta ƙi ya" Yaya Hamma ya dubi wannan matashin, ya dubi Daso wacce ta turɓune fuskarta kamar bata dariya. "To jeka zata zo yanzu. Kuma ni Hamma na baka damar zuwa zance wajen Daso Manga daga yau kuma yanzu. Daso tashi kije Manga zai yi magana dake" Nasan ganin rashin wasa gami da murtukewar fuskane yasa ta bishi ba dan ranta ya so hakan ba. Tafiyarta ke da wuya Yaya Hamma ya ce. "Bani labarin abinda yake damun zuchiyarki. Nayi miki alƙawarin magance miki matsalar duk girmanta" A'a Yaya Hamma babu komai. Ni dai inaso gobe zan je garin Kano. Amman nayi maka alƙawarin kwana biyu rak zanyi zan dawo." Da sauri ya kalleni har tsoron da yake son ɓoyewa ya kasa ɓoyuwa. "Kano kuma, ba dai wajen tsohon mijinki kike son zuwa ba, ko ganin yaranki ba? Kinsan yin hakan a wannan halin da kike ciku ka iya fama miki ciwon dake zuchiyarki" Da sauri na katseshi da cewa. Ko ɗaya ba abinda zai kaini Kano ba kenan. Akwai wani shiri da nake son in yi ne a can Kanon. In abun ya tabbata kaine mutum na biyu da zan faɗa ma bayan Daso" Ajjiyar zuchiya ya sauke yace. "Au ashe Daso ta fini matsayi a wajenki? Sai ta sani kafin ma in sani ko. Nagode" Yanda ya turɓune ƴar kyakkyawar fuskarshi sai ya bani dariya ainun. Ba haka nake nufi ba. Sabida ita ɗakunmu ɗaya da'itane. Amman kana da matsayi a wajena gaya. Ko tafiyar nan da zanyi gobe babu wanda na sanarma sai kai. Sai mun koma gida zan sanarma da Yafendo" Daɗi yaji sosai, sai kuma naga damuwa ta maye gurbin daɗin. "Allah yasa ba ƙauyenmu bane ya isheki kike son komawa maraya ba, sai da muka shaƙu dake kike son ki gudu ki barmu da kewa." Daso ce ta dawo ta zauna jagwab a gefena tana rishin kuka. "Ni Yaya Hamma bana son Manga. Bazan iya rayuwar aure da abokin Chubaɗo ba, gani zanyi kamar naci amanar Chubaɗo ne. Gashi kai kace ka bashi izinin zuwa zance, kuma kab garinnan waye baisan zafin kishin matar Manga ba. Ni ban shirya jefa rayuwata a cikin haɗari ba gaskiya " Dubanta yayi ranshi a bace, ko me ya tuna oho sai ya shiga aikin rarrashinta gami da yi mata nasiha. Mijintane dai ta rasashi har abada, ya zame mata dole yin sabon aure ko ba dan sha'awa ba ko dan tsira da mutunci. Ya ɗaura da cewa. "Kuma kinsan Baba ba zuba ido zaiyi ya barki kita zama a gabanshi babu aure ba ko. Lokacin da zai matsa miki da fito da miji nake jiye miki, dan in baki fitarba al'ada zata haɗaki aure da wani ɗan uwanki ko kina son hakan, ko bakya so. Ni abinda nake jiye miki kenan. Sannan Manga kab Rugar nan ansan mutumin kirki ne, gashi da yawan shanu, kuma jarumine sosai. Ko wacce bafulatana burinta auren jarumin namiji." Zaman dandalin dai haka muka ƙareshi babu armashi, Yaya Hamma ya mayar damu gida. Muna shiga a daren na sanar ma Yafendo inaso zanje Kano in Allah ya kaimu gobe, kwana biyu zanyi. Sai da ta ɗanyi jim kamar ba zata yarda ba, kamar tana son tambayata Allah ya soni bata tambayeni ba, sai cewa tayi dani. "Allah ya kaimu goben cikin rayayyu, sai ki shirya da wuri tafiyace mai nisan gaske" Da tunanin tafiyar na kwana a raina harma da mafarkin wai naje amman ban samu Uwani ba sai Hafizu mijinta. Washe gari tun asussuba nayi wanka. Ina yin sallah na fito da ƴar jakata ta hannu da kuɗaɗena a ciki. Kaya ko kala ɗaya ban ɗauka ba, nayi musu sallama akan zan biya wajen Dada da Boɗdo mu yi sallama. Daso ce ta fito domin yi mun rakiya. Muna fitowa muka ci karo da Yaya Hamma a zaune a bakin wata bishiyar darbejiya yana kallon ƙofar gida yaga yaushe zamu fito. Ba Daso ba ni kaina nayi mamakin ganinshi a wajen. Dan sai da nayi turus. Tasowa yayi ya nufo inda muke. "Yaya Hamma kaine da sassafe haka a ƙofar gida, zaman me kake yi a wajen?" In ji Daso kenan. Dariya yayi mata kawai kafin yace. "Tunda dai Allah ya ƙaddari ganawarmu ai shikenan. Babu gaisuwa sai tuhuma ko? Da fatan kun tashi lafiya" Muka amsa a tare, sannan mu ka gaisheshi cikin girmamawa. Gidansu Yaya hamma muka soma zuwa. A ɗakin Yafendo muka zauna, a gurguje mu ka gaisa na sanar mata inaso zanje birni amman kwana biyu zanyi. "To Allah ya dawo dake lafiya. Hamma sai ka kaita har tasha ka tabbatar motarsu ta tashi kafin ka dawo. Allah ya tsare. Hama da Boɗɗo suna garken shanu kuje ku samesu ko? Ke kuma Daso kizo in kin taso tallan Nono zamu yi magana muhimmiya dake" Kan Daso a sinne ta amsa da "To Yafendo" A garken shanu muka yi sallama da Hama da Boɗɗo. Sai adda'a su ke yi miki, daga nan sai wajen Dada. Ni da Daso ne muka shiga, Yaya Hamma fur yaƙi shiga yace Baffa faɗane dashi bai fiye son baƙi suna shigar mishi gidanshi ba. Mu ma muna shiga ya taremu harda sanda kamar zai dokemu. "Kai ku tsaya nan kar ku sake ko taku ɗaya a wajen" Ya faɗa da fillanci, Daso ce ta fassaramun abinda yace. Wannan kalma daya faɗa kamar ance Dada ta fito ta duba sai firit ta fito daga bukkarta. Su Cubu kuma da su Yusufu suna tsakar gidan, suna aikin dafa madara. Da sassarfa ta iso inda yake tsaye. Wallahi ɗaga sandar shi yayi kamar almara sai ya kwaɗa mata a goshinta jini ya yayi tsartuwa har a hijabina" Cikin hargagi yake yi mata magana da fillanci. Hannunta ta dafe da goshinta ta yi saurin juyawa, na fahimci umarni ya bata. Yusufu da Cubu ne suka yi kanta Cubu ta riketa zuwa ƙofar bukkarta. "Ku je Jabu. Zan dinga zuwa dubaki. Na mancene ban sanar miki ba ya kafa dokar kar ƙafarki ta tako mishi gidanshi" Da yarbanci tayi mun Magana. Ajjiyar zuchiya na sauke ina hango irin yadda sandar ta sauka a goshinta, ba tare da wani babban daliliba, ko da dalili addini ya bada umarnin a daki mace har a zubar mata da jinine? Ko da ma suna da ƙarancin ilimin addini, rayuwarsu a kiwo da tallar Nono take ƙarewa. Ji nayi na sake jin ƙarfin guiwar hukuncin dana yanke dan cire Dada a cikin wannan uƙubar. Hawayen daya zubomun nake shirin gogewa Baffa ya ɗaga sandarshi ya sauke mun a kafaɗata, zafin ya ratsa dukkan ƙasusuwan jikina kau,. Kafin in tantance tsakanin mamaki da tsoro naji Daso tayi ihu ta jani mun rufa waje a guje. A guje muka wuce Yaya Hamma. Sai biyo mu yayi da sauri yana tambayar ba'asin abinda ya haddasa gudun. Daso ce ta bashi labarin abinda muka tarar. Ni kam hawaye kawai nake sharewa ina kallon mayafina da jinin Dadana a jiki, sanadiyyar zuwa ganinta kawai aka zubar mata da jini. "Jabu kiyi haƙuri. Mu kanmu mun rasa yanda zamu yi mu tsamo Dada daga cikin halin da take ciki a wannan gidan. Amman abinda nake so dake shine dan Allah ki taya ta da adda'a, kuma zan baki shawarar kada ki sake zuwar mishi gidanshi, Dada zata zo har inda kike ta dubaki. Kar hakan yasa in kika tafi ki ƙi dawowa, hakan ka iya jefata a halin da yafi wanda take ciki yanzu. Zamanki tare damu zai iya kawo mata sauƙi sosai, kece babba ke zaki dinga rarrashin ƙannenki, kinga Boɗɗo kullum a cikin kuka da damuwar da Dada take ciki take." Ajjiyar zuchiya na sauke kawai nace. Babu komai, nagode da shawara. Daso ku koma daga nan ni zan tafi" "A'a ai kinji abinda Dadanmu tace dan haka har sai na tabbatar da fitar motarku a tasha. Daso ki koma gida ke" A wajen mu kai sallama da daso. Ni dai har muka gama wannan gwajab_gwajab ɗin fita zuwa gari hankalina baya ma tare dani. Wai duk haka Aure yake cike da ƙalubale kowa da irin nashi? Oh ya Allah ka kawo mafita a zamantakewar aure, ya Allah ka ba ma mata mafita. Har muka shiga cikin babbar tashar Adamawa babu wanda yace da wani ƙala a tsakanin ni da Yaya Hamma, dukkanmu sai tubka da warwara kawai muke yi, tare da karanta wasiƙar jaki. "Fullo Kano ne, ko Kaduna, ko Zaria ga motar Haɗejiya?" Cewar ma'aikatan tashar da suka nufo kanmu har suna rige_ rige. "Kano zata je, nawa ne kuɗin motar?" Cewar Yaya Hamma, tare da cusa hannu a aljihunshi. "Nera dubu da ɗari biyu zata biya" Kuɗin ya zaro ya kirga ya basu, ni kuma ya miƙo mun dubu da ɗari biyar. Ƙin karɓa nayi, ya dubeni rai a ɓace yace. "In baki karɓaba zaki barni cikin damuwa, da kokontan dawowarki rugar mu. Ni kuma dana tuna zaki iya ƙin dawowa, ko zaman rugarmu ya isheki take sai inji fargaba ta dirarmun. Jiya ɓarawon baccine ya ɗebeni shima cike da mafarkai akan tafiyar taki. Ungu kuɗinnan ko tsaraba kya yi musu" Nagode sosai Yaya Hamma, in sha Allah bazaan wuce kwana biyun ba. Kuma dan Allah ka je ka dubo Dada, ko a ɓoye ne ka kai mata magani, kai mata bayani kwana biyu zanyi" Yaya Hamma bai bar tasharnan ba har sai da ya ga fitar motarmu. Sai da motarmu ta yi nisa sosai na dena hango hannun Yaya Hamma a sama yana yi mun Adabo., ban dena waige ba har sai da na dena hango shudiyar rigarshi, Ajjiyar zuchiya na sauke na lumshe idanuna ina tunano yanda Baffa ya kabɗama Dada sanda. Wannan dalilin ne yasa kullum in zanga Dada sai in ganta cikin rashin guzari da rashin walwala, kullum cike take da tunani. Ta haɗu da azzalumin miji mai kafiya, tallar Nono ya cinye mata lafiyarta da kuzarinta. A shekarunta ya kamata ace tana zaune a nutse yaranta na hidinta mata, ba wai tai ta fita tallar nono, kuma mijinta na cin zarafinta harma da fitar mata da jini. Wallahi da Baffa zai iya amincewa in fanshi tallar Nonon Dada, da tuni na famsheta na zama ƴar tallar Nono kamar yadda ya zama al'adar matan fulani musamman mazauna rugage. Ya zame mun dole in yi duk abinda ya dace dan ganin na kawar ma da Dada Ƙwallar data daɗe tana zuba a idanunta. Gaga_gaga haka mukaita cin hanya, azahar, la'asar sai dab magriba muka shiga garin Kano, a unguwa uku muka sauka, ina fitowa titi na samu Bus har ƙofar layinsu Uwani. Na ko yi sa'a tana gida, tana tsakar gida tana kwasar tuwo Hafizu kuma yana shanya kayan yara a igiya. Tana ganina ta sau marar hannunta ta miƙe a zabure. "Iyabo kece haka afujajan?" Tana faɗin haka na fashe mata da kuka a tsakar gidan kamar ƙaramar yarinya. "Uwani jata kuje ciki maza" Cewar Hafizu. Hannuna Uwani ta ja muka shiga ciki, wallahi na fi minti talatin ina kuka take zazzaɓi mai azabar zafi ya rufeni. Uwani da Hafizu suka rufu a kaina suna ta rarrashina da ƙyar na haɗiye kukan nawa bakina na ambaton Allah. Ganin na ɗan samu nutsuwane Hafizu ya fita ya bamu waje. "Kawata lafiya kuwa kinga yanda ki kai baƙi kika rame kuwa? Gabaki ɗaya kin koma wata ƴar ƙauye, meke faruwa haka?" Cikin shessheƙa nace. Labarin da tsayi Uwani, amman bari in rama sallolina sai mu tattauna tunda abinda ya kawoni wajenki kenan" Ina gama faɗar hakan na miƙe jiri na kwasheni na fito tsakar gidansu dan kama ruwa da alwala. Uwani kuma taci gaba da aikin tuwonta, ina kan yin alwala yaran Uwani suka shigo gidan da sallamarsu. Matar gidan buɗar bakinta tace "Wannan wacce iriyar rashin tarbiyyace zaku shigoma mutane gida da gudu, kalan ku zubar mun da miyar da ko kayan ɗakin uwarku in an siyar bazai siya miyar ba?" Yaran su kai turus, ni dama nasan irin matsalolin da Uwani take fuskanta a gidannan shi yasa ban yi mamaki ba, gashi uwani ta kasance kamar zawayi wajen rashin haƙuri ai kuwa nan ta tanka. "Maman Shamsu kenan. Baƙin cikin ki takashinki zai koma da izinin Allah. Ni Uwani nafi ƙarfinki, kuma in mijinki yafi nawa mijin kuɗi, ai ni na fiki more aure tunda mijina bai taɓa zagin iyayena ba. Kuma bai taɓa korata da watan azumin ramadana ba, dan haka ki iya bakin ki" A mugun zafafe Uwani tayi maganar cike da hargowa. Yaran na kaɗa ciki dan gudun kar su kantamo kalmomin da suka shige shekarunsu. Da Uwani da maman Shamsu sun ci uwar sabada har sai da mazajensu suka dawo daga masallaci suka raba wannan ja'iba, dan wallahi na kasa riƙe Uwani sam, har zani Maman Shamsu ta fincike mata ya rage daga ita sai gwari na tsuma ( siket ɗin ciki). Ɗayar matar gidance ta ɗaukoma Uwani zanin ta ɗaura. Baban Shamsu cikin son bin goyen matarshi ba tare da bin ba'asin abinda ya faru ba yace. "A ɗayan biyu ya kamata ko ku ku bar gidannan, ko kuma mu tashi mu bar muku gidan. Wannan bala'in yayi yawa dan watarana wannan jarababbiyar karyar matar taka zata iya illatamun mata'" "Karya kace mata Ƙasimu? Uwani ba karya bace tunda bata leƙen mazan mutane in sun shiga bayan gida. Uwani Iyabo ku shige ciki kar ku tanka musu" Shigewa mu ka yi mu ka barma Hafizu faɗan. Matan gida sai ihu suke yi. Nifa harna rama sallolina ba'a dena gwabza habaice_habaice ba. Wannan ta jefa ma wannan, waccan ta rama, Uwani na tsaye a bakin ƙofa riƙe da labule sai ɓarin zance take ta faman yi. Yara kuma sai cin tuwonsu suke yi a yinwace." Uwani dan Allah ki rabu da Maman Shamsu ki shigo mu tattauna matsaloli" labulen ta saki muka shige uwar ɗakinta duk muka yada zango a kan katifa" Wai Uwani me matarnan take nufi dake ne haka?" "Sharri mana, baƙin ciki take yi mini. Jiya jiya fa na kamata tana barbaɗa mun garin magani a ƙofar ɗakina, kinga ɗauki babu daɗin da mu kaita yi kuwa? Mune har gidan mai unguwa fa. Amman kinga ta sake takaloni" Ajjiyar zuchiya na sauke . Labarin duk matsaloli na ba uwani, da ƙudirina da dalilin zuwana wajenta" "Lallai rayuwar mata cike take da ƙalubale mai tarin yawa. Wata matsalarta uwar miji irinki, wata matsalar ta ƙannen miji, wata jarabawarta maƙotane marasa ƙaunarta irina. Wasu dangin mij, wasu matan maƙota, wata ma abokin mijina, ko matar abokin mijinta sune matsalarta, banda kishiya da shegiya facala su ba'a lissafinsu ma. Na tausaya ma Dada aimun. Kuma ya kamata ku yaranta ku haɗe kai lallai ku nema mata takaddarta. Iyabo amman ramar da kika yi da sauyawarki ta ban tsoro" Hawayena na share. Uwani ƙauyene fa sosai can inda na koma. Babu ruwan famfo, sai wata rijiya guda ɗaya jol anan ake ɗiban ruwa, ba wutar lantarki, babu sabis ɗin waya, ba titi, amman suna da makaranta, sai dai al'ummar cikin ƙauyen aikinsu kenan kiyo, matansu kuma tallar Nono, suna da ƙarancin ilimin addini, ai dole ki ganni haka. Kuma jinya nayi magashiyyan sai an ɗaga sai an ƙwantar" Mun jima muna tattaunawa, sai da mu kai sallar isha mu ka ci abinci sannan Uwani ta zura mayafi muka nufi gidan Hajiya Salamatu. "To naji bayaninku. Amman Uwani kin mata bayanin komai da komai dai ko?" Cewar Hajiya Salamatu tana hakimce taci gwala_gwalai kunne da wuya, da tsintsiyar hannu. "E Hajiya na yi mata bayani. Sai dai itama bata da kuɗi kamar dai ni. Amman Hajiya in muka je can za'a cire a kuɗin aikinmu har mu gama biya. Mu ba ma daɗewa zamu yi a can ba shekara uku ya ishemu, dan da ita Iyabo shekara biyu ma tace" Hajiya tayi dariya tare da girgiza kai. MRS BUKHARI 3064127935 Buhari Ibrahim Ladan First bank Sanya nera 500 ɗinki kuɗin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan. Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. Ƙarƙashin Amila Foundati [8/6, 1:56 PM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE LITTAFI NA BIYU 1 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* Iyabo Motarmu na dira a tsaha idanuna su kai tozali da kyakkyawar fuskar Yaya Hamma. Yana jingine a jikin wata Bus ya ƙurama motarmu idanu bai ƙibtaba, bai kawar da kanshi daidai da na sakan guda ba, har sai da yaga na fito a cikin motar. Da sauri ya nufoni fuskarshi ɗauke da yalwataccen murmushi, murnarshi ta kasa ɓuya. Yasa hannu ya karɓi ledar kayana. "Jabu tunda na shigo tasharnan zuchiyata bata dena dokawa ba har sai da na ga sakkowarki a cikin motarnan. Wata zuchiyarma ce mun take yi baza ki dawo garemu ba kwata_kwata" Ɗan murmusawa nayi kawai nace. Yaya Hamma kenan, na gode da kulawa, amman kafin ma in tafi na sanar maka zan dawo." A jere muka fito daga cikin tashar, a bakin titi muka samu motar Girai muka shiga, wata kwaraɓaɓɓiyar Bus mara gudu muka samu. Bayan tafiyarmu ta ɗan yi nisa sai nace dashi. Ni ko ya jikin Dada Yaya Hamma?" Wannan tambaya tawa farad ɗaya saita sauya fuskarshi, daga farin ciki izuwa ɗaurewar fuska, harma da alhini. Lamarin daya dagula jinin jikina kenan, ruɗewar da nayi da yawa ne yasa yace dani. "Ki kwantar da hankalinki Jabu. Bawa baya iya tsara ma kanshi yadda zai rayu. Nayi imani da hakan na faruwa Al'umma babu mai zubar da hawaye. Bayan tafiyarki abubbuwa manya sun faffaru marasa daɗin labari. Amman bazan baki labarin komai a cikin motar haya ba. Kiyi haƙuri in mun je gida zaki ji komai" Bai daina rarrashina ba har muka iso Girai. Ni dai ko da muka shiga akori kura bana iya ko magana sai fargaba da nake cikinta. Jikina sai bani yake yi Dada ta haɗiyi zuchiya ta mutu ne ƙila bayan tafiyata, ko kuma maƙetacin mijinta ya kasheta. Da waɗannan tunane_tunanen muka shiga cikin Jaɓɓi lamba. Sai gamuwa da mata masu tallar nono muke yi Yaya Hamma gidan su Dada zaka kaini, zan tsaya a ƙofar gida sai kai ka shiga" Ƙuramun idanu yayi, sai naji idanun nashi sun yi mun kaifi ba shiri nayi ƙasa da nawa idon, tare da sauraren amsar da zai bani. "Dada bata gidanta, tana gidan Baffa Musa, ki bini kawai in kai ki" Ai jin haka yasa na kuma tsurewa har hawaye sai da ya zubo a idona. Tafiya muke babu mai cewa da ɗan uwansa ci kanka har muka isa gidan Baffa Musa, tafiyar ƙafa ce mai mugun nisan gaske. A ƙofar shiga gidan naci karo da Burodami Debisi shi da Jatau. Sai nayi turus ina dubanshi cike da maɗaukakin mamaki. Shi kuma cikin sanyi yake kallona irin kallon da naso in samu irinshi daga gareshi a shekarun da suka shuɗe, shekarun da wutar sonshi ta kusan ƙone mun rayuwata. Sai a yanzu da bana buƙatar kowa a cikin rayuwata ne, zai dinga jifana da irin wannan kallon? Ko zan iya ba maza wata damar, babu Burodami Debisi a cikinsu, zaifi mutumci ya riƙe matsayinshi na wa gareni "Iyabu Ekabo ( Sannu da Zuwa) Burodami Debisi yaushe a gari?" Na tambayeshi da yaren hausa, babu yabo babu fallasa a fuskata. Jatau yace. "Ai tun ranar da kika yi tafiya shima ranar yazo. Tare muke ta zuwa kiwon shanu" Da mamaki na dubeshi, kuma na yaba ƙoƙarinshi daya iya har kwana biyu a ƙauyenmu. "Mu je ciki Jabu, ki ga halin da Dada take ciki, naga kamar kin sha'afa" Cewar Yaya Hamma da muryarshi a kausashe har ɗan rawa take. Wucewa nayi cikin gidan, Yaya Hamma na biye dani a baya, su Burodami Debisi na biye dashi har zuwa cikin bukkar Goggo matar Baffa Musa. A kwance na tarar da Dada kanta naɗe da bandeji, sai kuma hannun damanta dana ga an ƙulle da tsumma, ga kara an jera mata kamar mai karaya. Sai numfarfashi take fitarwa, Boɗɗo na gefenta a zaune, su Yusufu, da Cubu duk suna kewaye da'ita, harda yaran Baffa Musa waɗanda suke gidan miji, Yafendonmu Jabu, da Yafendo kaɓoji mahaifiyar su Yaya Hamma, da Yafendo A'i suna wajen duka. Kuka kawai na fashe dashi domin na rasa ma abinda zance, bansan wa zan tambaya ya bani amsa ba, kowa a cikin damuwa yake. Boɗɗo ce ta dawo kusa daf dani ta riƙe hannayena biyu. Meke faruwa da Dada Boɗɗo, naga hannunta kamar karayace ma?" Baffa Musa ne yace. "Abinda ya faru kusan sanadiyyarki ne Jabu. Wannan ƙiyayyar da mijin Daso yake yi miki abune daɗaɗɗe sosai. Kuskuren da ita Daso tayi shine data yarda da sharaɗinshi kafin ya aureta. A lokacin da mahaifinmu Allah ya jiƙan rai ya matsa ma da Daso kan a cikin gwarazan samarin da suke neman aurenta za'a saka shaɗi, a lokacin shaɗi gwarazan mazan fulani suke yi su auri mace, dole sai namiji ya nuna jarumtarshi. Aka saka ranar shaɗi, Allah cikin ikonshi sai mai nagge yai nasarar cinye wannan gasa ta neman auren Daso. Gashi matashi mai dukiya, dan Allah ya albarkaceshi da tarin shanu a lokacin. Amman mutumne shi mai zuchiya da kafiya akan ra'ayinshi ko mai muninshi. Duk da wannan kusan ɗabi'ace dake gudana a jinin ko wanne bafulatani, amman na mai nagge yayi yawa. Bayan anyi aure kafin ta tare sai yake sanar mata shi mutumne mai tsananin kishi shi baya son ya saka ɗiyarta ƴar margayi a idanunshi sam, ta yi mai alƙawarin zata kiyaye mishi hakan, amman bazai hanata zuwa ganinki ba, bai kuma yarda yaranshi suyi zumunci dake ba. Ita kuma Daso cikin rashin sanin girman furucinshi sai ta amince mishi da duk abinda ya gindaya. Duk da dai ba'a musu dashi. Jabu daga ranar da yar mahaifnki Toyosi ta ɗakkoki ta kawoki garinnan dan kiga dangin mahaifiyarki, bayan tafiyarku sai da igiyar auren Daso ya kutsure, ta fuskanci tashin hankali, da faɗa sosai harda duka ma a wajen mai Nagge kafin ya korota gida. To shekaran jiya kinje mishi gida, a gabanku ke da Daso ya fashe mata kai. Bayan ya rakaku da gudu sai ya rufeta da duka. Ana cikin wannan hali ranar ko tallar Nono ta kasa zuwa. Sai ga Debisi shima da yamma lis. Zuwanshi ne yai silar da kika ga Daso a kwance tana jinya. Hamma gashi shi yaita kai kawo akan nema mata lafiyarta. Debisi kuma da Jatau suka kaita asibitin Girai aka duba lafiyarta. Wai hawan jinine ma da'ita a yanda su suka ce. Kinji abunda ya faru, amman kuyi hakuri wata rana fa sai labari, masu ba da labarin ma wata rana basu. Haka zamu shuɗe kamar yadda magabatanmu suka shuɗe. Kuka mai taɓa zuchiya na fashe dashi kawai. Wannan zalunci da mai yayi kama, yama za'ayo a raba uwa da ɗiyarta ɗiyar ma ta fari marainiya bugu da ƙari. Tsit ɗakinnan yayi bakwa jin komai sai sautin kukanmu ni da ƙannena da suka kewayeni suna rarrashina. "Jabu ki dena wannan kukan. Ki yafe mini kinji? Yarintace tasa bansan girman sharaɗin da mai nagge ya gindayamun ba, ba dan bana sonki bane na amince mishi ba. A cikin yarana kab nafi jinki fiye da kowa, kasancewarki marainiyar yarinyar da bata taso a gaban mahaifanta ba. Bugu da ƙari soyayyar Toye kanki ta koma kacokam." Hannunta nayi carab na kama, idanu ta lumshe wasu hawayen nadama suka gangaro mata. Mayafina nasa na goge mata. Baffa Musa ne yace. "Daso baki da lafiya bai kamata ki yawaita magana ba. Hutu kike buƙata. Na faɗa ma Jabu wannan labarinne domun tasan abinda ke gudana, ba dan in tashi hankalinki ba. Kai kuma Debisi duk sanda zaka zo wajen Jabu, ka sameta a gidan Yafendonta, ka sanarma Toyosi itama. Jabu ku tashi ku koma can gidan Yafendonku, ki samu ki huta" Ba haka naso ba, so nayi su barni in yi ma Dada jinya. Amman Baffa Musa yaƙi fur sai cewa yayi ma dinga zuwa dubata, matanshi zasu kula da'ita. Muna tafe a hanya amman tunani ya cika kaina, damuwa tayi ma zuchiyata yawa, ina neman wanda zan kwanta a kafaɗarshi in ci kuka ko zan samu salama. Gwadabe ne ya faɗo mun, tunashi kawai da nayi wallahi sai na tsinci kaina ina murmushi kawai. Tare duka muka shiga gida. Ni da su Daso wacce tunda na dawo naga ta fita sha'anina. bukkarmu muka shiga, na nemi waje na zauna jigum. Yaya Hamma ne ya shigo hannunshi riƙe da kayana. Yana shigowa sai naji Daso ta sau siririn tsakin da ba kowa ne zai ji ba. "Ga kayanki Jabu. Ku kuma ku bamu waje zan yi Magana da Jabu" Su Cubu duk suka miƙe suka fita, banda Daso wacce kwanciya take shirin yi. Sai da ya yareta kuma da faɗa naga yana magana. Kuka kawai naga Daso ta fashe dashi ta fice fuu. Ni dai ba ta fishin Daso ma nake ba, ta kaina nake yi. Zama yayi a ƙasa yana fuskantata. Idanu ya zubamun yaƙi cewa dani komai, yaƙi kuma ya dena kallona. Ni kuma duk sai na tsargu. Jatau ne ya leƙo. "Jabu ki zo Debisi yana son zaku yi Magana, yana gindin bishiya, ki je da tabarma, ga fura Hari ta dama sai ki tafi mishi dashi" To" kawai na iya cewa, ya saki asabarin yayi tafiyarshi. Yaya Hamma kuma naga yayi ƙasa da kanshi kawai yana wasa da layar dake ɗaure a tsintsiyar hannunshi" Yaya Hamma bari in je in dawo, tunda naga kamar baka son yin maganar da kace zamu yi" Ɗagowar da zaiyi sai naga idanunshi sun rine, jijiyoyin fuskarshi sun yi burɗun_burɗun. Gabana ya yanke ya faɗi ganin yanda cikin ƙanƙanin lokaci na ganshi a cikin wani irin yanayi. Cikin kaurin murya mai cike da karaya yace. "Shikenan gobe zan dawo, nima zanje gida in kwanta jiri nake ji" Haka kurum sai banji daɗin ganin shi a sabon kamanni ba. Kafin in gama tubkewa ya fice bankai ga warwarewa ba. Jikina a mace na fito tsakar gidan. Tabarma da damammiya fura Hari ta miƙo mun nasa hannu na karɓa. Har na kai ƙofar fita na juyo na kalli Boɗɗo nace. Boɗɗo ku jirani in je in dawo. Inaso zamu je gidanki akwai muhimmiyar maganar da nake son mu tauna" Ina faɗan haka sai naga Daso ta zare idanunta, firgici ya bayyana karara a fuskarta" Ficewa nayi waje. A tsaye a gindin bishiya na hango Debisi yana kallon garken shanun da suke wucewa. Kurama juna idanu muka yi, ina daga tsallake ina jiran shanun su gama wucewa" Zuchiyata ce naji tana bugawa da ƙarfi, idanun Debisi naji sunyi mun kaifi. Na so Debisi so na haƙiƙa, soyayyarshi ta wahalar da rayuwata, dan zuchiyata bata iya son abu ba, in zata so abu da gaske take sonshi, haka kuma ban iya ƙin mutum ba" Bamu dena kallon ƙudan da muke ma juna ba har sai da garken shanunnan suka gama wucewa. A hankali na isa ƙarƙashin bishiyar. Carab ya amshe ƙwaryar damammiyar furar dake hannuna. Na shimfiɗa tabarmar dana fito da'ita, tare da cewa. Bismillahi Buradomi ka zauna" Murmushi yayi mun, irin wanda ada nake mafarkin ganin yanai mun. Banda a yanzu dan tuƙuƙi naji zuchiyata nayi mun. Kuma ina fatan ba cewa zaiyi sona yake yi ba, dan zan iya zaginshi tsab, laifinshi mai girmane a gareni, babu abinda zai iya faɗamun in yarda ba yaudara bace" Waje na samu na zauna kamar yadda yai mun izini. Shiru ne ya biyo baya na tsawon minti shida kafin yace "Bansan ta inda zan soma ba Iyabo. Gashi zuwan nawa ya haifar da matsala mai girma, ina mai neman gafararku baki ɗaya. Amman kafinnan me kika je yi a Kano, sannan wannan ramar duk ta rabuwa da Gwadaben ce, ko kuna cikin wata damuwane?" A jijjere yayi mun tambayoyin da na yi jim, ina cinka cinkar wanda zan sona amsawa a cikin zuchiyata. Sai na sake jin amon muryarshi yana cewa "Da zan baki shawara, da nace ki shirya ki bini mu koma Kano. Tunda kika baro Kano kika barmu cikin kewa da alhinin rashinki. Nawa kuwa yafi na kowa. Kuma a kwana biyu kacal da nayi a rugarnan na tabbatarma kaina rayuwarki ba zata taɓa yi miki daɗi ba. Ke da kika taso a maraya, ga hasken lantarki, ga ruwan famfo, ga makarantu, ga titina, ga_ga_ga. Amman anan fa babu abunda suka sani sai kiwo da tallar nono, ace kamar Dada tallar Nono itama take zuwa yi, su Ɓodɗo ma tallar suke ɗauka fa" katseshi nayi ta hanyar cewa. Tambayarka ta farko gareni shine. Naje Kano ne nayi fasfo zan tafi ƙasa mai tsarki da izinin Allah neman kuɗi. Tambaya ta biyu kuma. Ciwo nayi mai tsayi shi yasa na rame. Gwadabe kuma yana ɗamfare a raina tsaiwar numfashinane kaɗai ka iya kawo ƙarshen soyayyar Gwadabe. Batun rashin iya zaman rugarnan kuma. Zan iya ko dan Dada, da ƙannena. Bana jin komai na dangane da kewar birni, ko ƙyale_ƙyalen dake cikinta. Ni babu abinda a halin yanzu yake burgeni. Nafi samun nutsuwa a haka" Ashe ni na kasheshi da namaki ban sani ba. Sai da na juyo naga bakinshi a hangame yana kallona, da halama ya ɗan jima yana kallon nawa "Saudiyya fa kika ce zaki je neman kuɗi Iyabo?" Ya faɗa a ƙagauce da son jin amsata. E Saudiyya da izinin Allah, Lokaci kawai zamu jira." " Da izinin wa zaki tafi Iyabo, me yasa Kano bata isheki neman kuɗi ba har sai kin dangana da ƙasa mai tsarki, sannan me yasa baki yi tunanin Aure, ko komawa makaranta wanda nasan yana daga cikin burukanki na rrayuwa ba?" Ya sake jejjero mun wannan tambayoyi cikin ɓacin rai a wannan karon. Baki na tsuke bance mishi komai ba. Tsawa ya daka mun wacce tasa ƴan hanjina kaɗawa. "Ba dake nake yi ba kin mun banza ba?" To ni kam Burodami me zance maka? A halin yanzu babu wani karatu, ko aure a gabana. Rayuwar mahaifiyata kawai nake dubawa, da mafarkin samar mata da sauƙin rayuwa. Ka dai taya ni da adda'a zaifi. Dan babu makawa zanyi tafiyarnan. In kaga banje ba Allah ne baiyi ba. Kayi haƙuri kar kace na bijire maka" Sai yayi shiru na wasu daƙiƙu kana yace. "Amman ba kya ganin in kika tsallake ƙasarki Najeriya, kika tafi wata ƙasar neman kudi. Ba kya ganin wasu zasu yi miki kallon da bai dace ba? Ballantana kinga ke bazawarace kina da ƴaƴa. Acan kuma baki san hannun waɗanda zaki faɗa ba" Hannu na gari zan faɗa da izinin Allah. Kuma wama zai san na tafi Burodami Debisi?. Kaga Dada tana cikin halin da ya kamata a taimaka mata. Kuma ni bazan wuce shekara uku ba zan dawo. Kafin in dawo amman sai na tabbatar da na samu dukkan abunda naje nema." Ajjiyar zuchiya ya sauke, yayi shiru yana kallona, ni kuma nayi ƙasa da kaina. "To batun aurenmu sai kin dawo za'ayi kenan. Ko kuwa zaki amince a ɗaura kafin ki tafi? Dan ni harna sanarma Baffa Musa sababin zuwan nawa. Yayi murna matuƙa da jin hakan" Wani kallo nayi mishi, wanda ko a mafarki banyi tunanin akwai ranar da zata zo da zan yi mishi wannan kallo ba. Aure a tsakaninnu babu shi har gaba da abada. Har gobe nice Iyabo mai ƙibarnan, wannan wacce sai da ka kwanta jinyar ƙiyayyarta. In ma mafarki kake yi ka farka" Ina dasa aya sai kawai na miƙe hawaye fal Idanuna. Takalmaa nake shirin sawa yayi maza ya miƙe shina. "Iyabo" Ya kirani da sauri. Cak na tsaya. Ban tafi ba, ban kuma juyo ba. Ina jiyo takunshi har izuwa daf dani. "Nasan kina sona Iyabo kar ki soma yaudarar zuchiyarki. A rashinane kika auri Gwadabe. Iyabo zan baki farin ciki irin wanda mafarki da hasashe ba zasu iya hasko miki ba. Duk duniya ba wanda zai soki sama dani, sai dai ya biyo bayana." Hawayena na share, tare da lumshe idanuna, zuchiyata kuwa sai aikin turiri take. Da ƙyar na haɗiyi miyau nace. Iyabonnance dai wannan mai ƙibar da kaƙi aurenta sabida wannan halitta tata. Ba canjawa nayi ba. Duk da nasan na zabge rabi da kwatan ƙibata, a sanadiyyar halin yau da gobe Ka sani kibata zata iya nunkuwa da kaso sama da hamsin akan na da wanda ka guje ni dominta. Debisi ina mugun girmamaka ne ma yasa harna tsaya saurarenka. Amman da ba dan haka ba ko kusa dani baka isa kazo ba. Maganar soyayya ko aure babu ita, dalilin da yasa ka barni ina budurwa. Dalilin ne dai yasa na barka bayan na zama bazawara" Ina dasa aya nayi shigewata cikin gidan. Duk a tsakar gida na tarar dasu, amman banda Daso. "Adda Jabu Yaya Debisi ya kawo miki wata ƙatuwar leda, tana wajen Adda Daso. Muma duk yayo mana tsaraba mai yawa" Ɗan murmushi na ƙaƙaro nace. Ayya. Ai Burodami Debisi ba daga nan ba ta wajen kyauta. Boɗɗo ku taso muje gidanki, dan acan nake son mu tattauna kamar yadda na faɗa miki ina da Magana da zamu tattauna daku. Ina zuwa bari in samu Daso in sanar mata" A cikin bukkarmu na sameta tayi tagumi sai aikin tunani take faman yi, dan bata san ma na shigo ba har sai da nazo daf da'ita. Ta ɗago fararen idanunta ta zuba mun su. Akwai damuwa sosai a tattare da'ita, wanda a tunanina baya rasa nasaba da kewar tsohon mijinta marigayi. Daso wai me ke damunki ne, ni tunda na dawo na ganki wani sukuku. Ko duk rashin lafiyar Dada ne?" Na jefeta da tambaya, tare da kafeta da idanu domin karantar yanayinta. "Ba komai abubbuwane sukai ma zuchiyata nauyi Jabu. Amman zamu tattauna zuwa dare" kai na gyaɗa mata kawai. To ni zanje gidan Ɓoɗɗo akwai maganar da zamu yi dasu duka" Kur ta mun da idanunta kamar mai karantar wani abun a fuskata, sai kuma ta ja numfashi tace. "Bari in zo muje, inaso dama inje wajen Hama, in yaso in kun gana tattaunawar sai ki same ni a ɗakinta" Hakan ko akayi, a hanya ne take labartamun Debisi ya kawo mun wata ƙatuwar leda, ta adana mun ita. Ni dai kai kawai na gyaɗa. Mun ci tafiya sosai kafin muka iso gidan. Matan gidan duk suna tsakar gida anata tuwon dare, wasu kuma suna wanke ƙoren tallar nononsu, Yafendnmu bata nan bata dawo daga can gidan Baffa Musa ba. Daso ta ya da burki a ƙofar bukkar Hama, tana zaune tana tuƙin tuwon masara, masararnan fara tas gwanin ban sha'awa. Da dariya da haba_haba muka kaisa da Hama kafin muka shige bukkar Boɗɗo. Bayan kowa ya nemi waje ya zauna, sai na yi gyaran murya na soma da cewa." Dukkanku kun fini sanin irin halin da Dada take ciki a gidan aurenta. Da irin matsalolin duka, da tsangwamar da Baffa yake yi mata. Ku yi haƙuri Baffa mahaifinku ne, amman nasan ku kan ku kunsan yana zaluntar Dada. A shekaru irin na Dada ai yaci ace ko da an daketa a baya, a yanzu a barta ta huta ko dan kaifin idanunku. Ga yawon talla, duk rauni da da gajiyar dake jikinta tana talle. Amman anan naga ku kamar talla wani abune na dole." Boɗɗo ta tari numfashina da cewa. "Talla tana cikin sharaɗin aurenmu mu kam. Domin da kuɗin nononnan zaki ɗauke nauyin ci da sha na gidanki, harma ki yi ma kan ki sutura da dukkan buƙatu. Su kuma maza aka barsu da kiwo. Sai dai wasu matanma suna fita kiwon su dawo lafiya. Dukan da Baffa yake ma Dada ni shine damuwata. Anan ɗakin mun sha zama domin tattauna wannan matsalar, rashin mafita ke sa mu yi haƙuri kawai. Amman zukatanmu na sosuwa ainun, hakan ya zabtare kima da darajar Baffa ta Uba a garemu. Domin mun fi son Dada sama dashi sai dubu babu haɗi" To ni dai ina da shawara, so nake zan tafi saudiyya neman kuɗi. In na tara kuɗi zan dawo, inaso Baffa ya saki Dada ne kawai. Ni kuma zan ɗauketa harda su Yusufu in sai mata gid, ta zauna ta ci moriyar haihuwa ko wanke_wanke ni zan dinga yi mata ko da nayi aure. Amman meye shawararku kune ƴan uwana?" Boɗɗo tace. "Da hakan zai faru wallahi Adda sai mun fi kowa farin cikin faruwar hakan. Ni da Amaduyal mu muka san irin wuya da dukan da Baffa ya dinga yi ma Dada. Har ɗaureta yake yi a jikin gadonta ya daketa ciki da waje." Anan suka sake fayyace mun halin da Dada take ciki a gidan aurenta. Kuma duk suka bani haɗin kai akan suma sun amince a saki Dada. Sai dai wani hanzari ba gudu ba, duk yawan shanayen Dada dake hannun Baffa bazai yarda ya bayar ba. Ni kuma a wannan lokacin sakin kawai nake buƙata ba shanayen banza ba. Sai da mu kai sallar isha a gidan. A ɗakin Yafendo muka haɗu mu ka ci abinci anata hira, maza kuma suna waje suna shan iska. "Cubu je ki kira Hamma a waje ya raka su Daso guda, kuma sai ku kama hanya tunda ga Yusufu sai yai muku jagora" fitar Cubu ke da wuya sai gata Yaya Hamma na biye da'ita. "Dada gani" Ya faɗa da murya mai kauri. Yarinyarshi dake hannun uwarshi sai ɗaga mishi hannayenta take yi halamar ya dauketa Hama ta miƙa mishi yarinyar ya ratayeta a kafaɗarshi. "Su Daso zaka raka gida tunda dare yayi ." Ɗan murmushi yayi kawai kafin yace. "To Dada su sameni a waje sai mu je. " A tsaye ya ɗan yi ma ƴar tashi wasa ya miƙa ta hannun uwarta ya fita. Muma mu kai ma Yafendo sallama muka fito, suma su Yusufu suka nufi hanyar komawa gida. Shiru_shiru mukaita tafiyar. Duk cikin mu ukun kowa da abinda ke azalzalar zuchiyarshi. Abun mamaki har muka isa gida ba wanda yayi ko tari. A ƙofar gidan muka haɗu da Jatau da Burodami Debisi sun kafa sun tsare suna jiranmu. "" Ƴar halak ta ƙi ambato ka ganta ma. Jabu mun fi mintu talatin muna jiranki anan wajen" Hannu Yaya Hamma ya miƙa musu suka gaggaisa, sai naga ya kuma haɗe ranshi. Ni da Daso dai muna tsaye, Allah cikin ikonshi sai ga Manga shima ya tawo taɗi shi da abokinshi. Yaya Hamma ne yai ma Daso jan ido ta je wajensu. "Jabu ki je ki saurareshi, ni zan jiraki a wancan wajen itaciyar, inason mu yi magana ne" Yaya Hamma ya faɗa a sanyaye. To Yaya Hamma" Iyakar abinda na faɗa kenan. Burodami Debisi yaima Hamma godiya, ni dai na bi bayanshi dai muka matsa gefe haka. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI CE Ina miƙa saƙon gaisuwa ga masoyana. Sister Khadija maidoki ina godiya. [8/7, 2:38 PM] +234 802 065 1487: NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE LITTAFI NA BIYU 2 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* "Gimbiya Iyabo sai wahalar da zuchiyata sonki yake ta yi. Ni na ɗauka dake zan koma Kano a matsayin matata fa, ashe abun ba haka bane. Ki tausayama masoyinki ki tsamoni daga cikin halin da kika sanyani, kaina bisa wuya, banda tuno baya. Kuma nayi imanin su Iyaa da Burodami kokodeen zasu yi alfahari da aurenmu Iyabo " Duk wannan maganar yana yinta ne cikin kyakkyawan lafazi mai taushi. Maganganunshi babu inda basa ratsawa a jikina. Sai dai kash ya makaro, dan banga abinda zai iya cemun in yarda dashi ba. Ina Mai baka hakuri ka fitar dani a zuchiyarka dan Allah. Nayi imanin a rashin samun yadda kake so a wajen matarka soja ne yasa kake son ni ka aureni" Da sauri ya fuskanceni sosai cikin kidima yace. "Wallahi bazan iya ba. Baki san irin azabtuwar da ruhina da gangar jikina suke yi bane shi yasa. Ki dena tunanin dan ban samu yadda nake so a wajen Yemisi bane na dawo gareki. Iyabo ina sonki" Ɗan guntun murmushine ya sufce mun ba tare da na shirya ma hakan ba. Zaka iya, tunda har na iya cire sonka a zuchiyata. Na rungumi soyayyar Gwadabe har kuma ya samu matsayin da babu wani ɗa namiji da zan iya bashi wannan matsayin. Kaga kuwa zaka iya, dan a baya sonka ya rufe mun idanu ta yadda bana ji bana gani. Ido da addini kaƙi fur a haɗa mu aure. Kaje ka auri sojar matarka siririya irin samburin matan da suke burgeka. Na roƙeka ka barni in auri namijin da yasan darajar ƙiba irin Gwadabe. Wanda zai dinga kammamani yana kuranta kyauna" Baki na tsuke nayi kicin_kicin. Daya isheni ma da magiya sai kawai na fashe mishi da kuka. Da ƙyar ya rarrasheni nayi shiru. "Shikenan Iyabo, zan sake baki lokaci. Ni gobe zan koma asubanci zanyi. Amman fa ki sani zan jiraki kije ki dawo sai muyi auren" Allah ya tsare ka gaishe mun da kowa da kowa. Banda matarka Yemisi, dan nayi imani batasan wajena ka tawo ba" Bai iya ce mun komai ba na yi tafiyata na barshi a wajen. Yaya Hamma kuma yana daga can gefe can gaba da inda su Daso suke tsaye. Dole ta gabansu zan wuce, hakan yasa saida na tsaya aka gaggaisa kana na Isa wajen Yaya Hamma Daso ta bini da idanu kawai. Zama nayi a gefen itacen da yake zaune, muka ƙurama juna idanu ƙur kamar zamu haɗiye junanmu. Idanunshi jawur harda kwantaccen hawaye marar yawa a cikin idanun nashi. Lumshe idanu yayi, yaja wani numfashi marar fassara a gareni, yai amfani da murya mai salon taushi da sanyi tarara wajen cewa. "Me yasaki kuka, kuma me Debisi yake nema a wajenki ne Jabu, na fahimci akwai babban sababin daya kawoshi rugarnan?" Ƙireni da idanu yayi. Nima ajjiyar zuchiyar na sauke. Na fayyace mishi ƙudurin Burodami Debisi a kaina. Na tsokata mishi ɗan labari akan cewar iyaye a baya sun haɗamu aure amman sai ya nuna baya ra'ayina. Amman na ɓoye mishi dalilin shi na ƙin nawa. Murmushi naga yayi har yanayin fuskarshi sai da ta sake. Gyara zama yayi yace. "To cika mun alƙawarina da kika ɗaukarmun akan kina dawowa zaki sanar dani dalilin zuwanki birni" Dariya na kwashe dashi, shima dariyar yake yi. Kwashe labari nayi na bashi. Da kuma dalilin da yasa zan tafi ɗin. Tashi ɗaya ya birkice har yana tsugunnawa akan guiwowinsa a gabana. Idanunshi suka cika fal da hawayen da suka kasa gangarowa. "Na roƙeki kar ki tafi Jabu ki barni. Shekara uku ban saki a idanuna ba, ai abune wanda ka iya kwantar dani. Ni zan siyar da saniyata in baki kudin a hannunki ki siya ma Dada gida, kiyi sana'arki da sauran kuɗin ki yi haquri ki janye wannan tafiyar dake shirin rabamu. In kuma ni kike so in mata duk abinda kike so a shirye nake. Yafendo uwatace, ina jin motsin sonta da tausayinta a raina. Jabu na roƙeƙi kar kiyi nisa damu, rayuka da yawane zasu jikkata" Mamaki ya kamani, to me Yaya Hamma yake nufi da wadannan kalami nashi? Ni ba yarinya bace na lura sarai tun zuwana yana ra'ayina. Amman ban tabbatarba sai jiya dana ga kishin Debisi ƙarara a idanunshi. Wannan kalamai nashi na yanzu sun ƙara tabbatarmun Yaya Hamma rainon sona yake yi. Kuma na fahimci Daso na tsantsar sonshi, Yafendo ma ta sani kuma tana fatan faruwar hakan. A duk sanda Yaya Hamma zai zo gida, sai Yafendona ta alaƙanta zuwan da Daso. Gashi matarshi ƙawarmu ce, mutuniyar kirki mai son jama'a. Kayi haƙuri ka tashi dan Allah yaya Hamma mu yi magana ta fahimta dan Allah " A tsugunne a gabana Daso ta iso ta sameshi. Numfashi ta ja tare da saurin yin turus, ganinta ne yasa ya tashi ya zauna. "Ki shiga gida Daso, ban gama magana da'ita ba. In muka gama zan rakota, ina buƙatarta tare dani" Fuu ta wuce har tana haɗawa da gudu. Tausayinta ya kamani, dan babu son da ya kai son maso wani ciwo, zafi ne dashi kamar zafin fitar rai daga gangar jiki. Mun fi awa ɗaya da rabi muna tababa tsakanina da yaya Hamma akan tafiyata. Bamu cimma matsaya ba Baffa ya fito ya korani ciki dan gaskiya dare yayi har ƙafa ta ɗauke magiya kawai Yaya Hamma yake yi tare da tambayata shanu nawa zai siyar ya bani kuɗin. Ko da na shiga bukkarmu a zaune ƙiƙam na samu Daso ta kurama aci bal_bal idanunta. Ledar gabanta ta turo gabana ina tsaye. "Ga saƙonki na wajen ɗan uwanki" Murya ba daɗi ta yi maganar. Ledar na ɗauka na zauna. A hankali na zazzaro kayan dake ciki. Kayan tea na gani, da macline da brosh, sai mayafai biyu, takalmi biyu da atampa ɗaya leshi ɗaya, sai zungureriyar wasiƙar da bani da niyyar karantawa. Biyu na raba kayannan cib na ba Daso, kayan tea ɗin kuma na ajjiye mana. "Ki riƙe abunki ni bana so" Wai Daso na yi miki laifine kike fushi dani. In akwai matsala ki sanar mun mana?" Na jefeta da tambayar ina ɗaga murya dan ta mugun ɓata mun raina ainun. "Hmmm" Shine iyakar abinda tace dani. Kayana na kwashe na mayar ko da na ɗane gado na kwanta Amman me? Sai bacci yace bani bashi. Tunanin Dada ya cakuɗe mun da tunanin furucin Yaya Hamma na ɗazu, da irin yanda duk ya kiɗime. Hasko mun da hoton Gwadabe da zuchiyata tayi sai hawaye ya soma tsiyayomun masu zafin gaske. Babala ta zalunci zukatanmu data ƙi amincewa mu rayu a tare. Nasan duk inda Gwadabe yake kuwa yana can zuchiyarshi a batse da kewata. A tsakanin ni da Daso babu wanda ya runta Washe gari sassafe ni da Hari muka gama duk aikin gida. Ina gama karyawa nai ma Yafendo sallamar ni zani gidan Baffa Musa. Acan na tarar mijin Dada yazo ɗaukarta, kuma abun haushin harta fito daga ɗaki ma suna tsakar gida. Da ƙyar na danne zuchiyata na bashi girmanshi albarkacin uwata da yake aure. Shi kuwa banza ya ba ajiyata, in kun tanka ya tanka. Har a kan fuskar Dada banga tayi farin cikin zuwan mijinta ba, fuskarta ma cike take da tsoro. Amman haka ya tusata a gaba suka tafi, ni ko da kuka na fice a gidan na dawo gida. Na tarar da su Yafendo sai dafa madara suke yi, taga na shigo da kuka kamar karamar yarinya dai. "Jabu lafiya kaddai Adda Daso mutuwa tayi?" Ganin yanda duk suka ruɗe suka yo kaina yasa na yi musu bayanin dalilin kukana. Yafendo da Hari ne su kaita rarrashina dai haka. Gaga_gaga haka rayuwa tai ta tafiya. Ko wacce rana kafin faɗuwarta sai hawayena ya zuba. Dada jikinta ya warware har ta soma fita tallar Nono. Sabida tsananin tausayinta yasa nake binta wajen sana'ar nonon nata. Sai tayi zamanta a gefen rumfa. Ni kuma ni zan zuba Nono in kai, in je in kwaso ƙworena. Munayin hakan ina jin daɗi itama tana jin daɗin hakan, dan karayar tata bawai ta warke sumul bane. Ƴan tsegumi suka sanarma da Mijin Dada ai ana ganinmu tare. Kwatsam muna kan siyar da Nono sai gashi ya zo dan ya zama ganau ba jiyau ba. Da ganinshi Dada jikinta ya soma mazari. Kwafa yayi kawai yaa bar tashar fu. Ranar dai haka muka ƙarashe kasuwarnan cikin taraddadi. Wannan shine silar da na dena bin Dada wajen sana'ar tata. Ta ɓangaren Hamma kuma shaƙuwar data shiga tsakaninmu shakuwace ta ban mamaki. Banda Dada da ƙannena,shi kaɗai nake gani ya yaye mun damuwata da kalamanshi masu sanya kuzari, gashi kullum sai naci tsire da lemun kwalba, Abunka da ƙauye tuni ƴan tsegumi suka tseguntama Hama ana ganin Hamma kullum da wata mace har dandali. Dan babu ranar da bama zuwa dandali, da Hama ta gane ai nice mijinta ke ƙwaƙwa, duk wannan far'a da haba_haba da take yi muni sai du ta dena. Har ta kai ta kawo ta dena kulani, ko na gaisheta ma da kyar take ka da baki ta amsa, harma abu ya zame musu rigima a tsakaninta da Boɗɗo. Daso kuwa tsakanina da'ita takun saƙane, taƙi ta yarda ba soyayya muke yi da Hamma ba. Tunda duk shakuwarnan bai taɓa cewa yana sona ko zai aureni ba. Ita kuma ma a lokacin har Baffa ya san da zaman Manga. Dan ance mishi zuwa kaka ya turo manya a gama komai. Ita kuma tayi tsalle ta dure kan cewar Allah ya kasheta bata son Manga. Baffa kuma yace ya bata kwana talatin ta fito da mijin aure in ba hakan ba ya aura mata Manga. Ni dai sai shirin tafiyata na sanya a gabana, nayi watsi da iskantakun Daso. Lokacin da labarin tafiyata ya shiga kunnen Dada bata ja ba, sai ma fatan samun nasara da tai mun. Baffa Musa ne yaso ya turje, amman su Dada suka haɗu suka tausheshi. Yaya Hamma dai ko hirar tafiyar tawa nayi mishi sai ya gimtse fuskarshi shi yasa ko zancan ma ni bana yi mishi, shima baya so, yayi juyin duniya in janye wannan tafiya. Ni kuma fur naƙi amincewa, har shanu biyu ya siyar da daddare sai ga kuɗi dumus nera na gugar nera har nera dubu ɗari cib Miƙo mun yayi nasa hannu na amsa sai naga kuɗine. Bayani yaimun akan siyar da shanunshi da yayi, duk dan kada in tafi. Ni kuma naƙi karɓa fur, na bashi hakuri tare da yi mishi bayanin na riga nasa Hajiya Salamatu ta kashe kudinta da ɓata lokaci. In nayi mata haka ban kyauta ba. Dole babu yanda ya iya haka ya mayar da kuɗin aljihun ƴar shararshi, tare da sauke kanshi ƙasa kawai. To ya akayi_ya akayi labarinnan ya je kunnen matar Yaya Hamma sai Allah. Nan ta da bori Boɗɗo na bani labarin irin rikicin da su ka yi ita da Yaya Hamma. Har sai da Yafendo ta shiga cikin lamarrin. Kuma jin abinda Yaya Hamma ya aikata yasa Yafendo ta fusata itama. Kun dai san fulani da maganar Shanu, dan tsabar ɓacin ran da Yafendo tayi ƙwace kuɗin tayi a hannun shi Yaya Hamman, tare da gargaɗin koma me zaiyi mun yayi mun ni ƴar uwarshi ce. Amman bata yadda ya sake taɓa shanu ba, waɗannan shanu gadon_gadone da suke fatan ƴaƴansu Hamman da jikokinsu, da haularsu masu zuwa suita gadansu. . Ana saura sati guda in tafi, sai Yaya Hamma ya soma rashin lafiya. Abu kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Tun yana zuwa kiwo har dai ya dena. To dake a ɗakin Yafendo yake jinyar tashi, ana saura kwana biyu in tafi sai na je dubashi. Ina shiga sai Hama ta bar duk abinda take yi ta dawo ɗakin Yafendo ta zauna. Harma tana shafan sumarshi a gabana dan inji haushi, shi kuma kunyata tasa ya ture hsnnunta. Ai ko abun ya mugun sokar zuchiyata ta yadda ni kaina sai da nayi mamakin yanda naji sautin kishin mutumin da bai buɗe baki ya furta mun kalamin so ba. Sai dai iya so da kulawa a aikace yana nuna mun. A furucine bai furta ba, kuma na fahimci nauyi abun yake yi mishi. Kunya da kawaici irin na fulanine ya hanashi furta mun yana sona. Shigowar Yafendo da fura a hannunta ne yasa Hama tashi ta dawo ƙasa ta zauna. "Jabu ga fura ki sha" Ta miƙo mun. Hannu biyu nasa na amsa nace. Use Yafendo. "Hama kin baro aikin ki kin dawo kin zauna? Maza tashi ki koma kan aikin ki, kinsan zaki je tallan nono fa" Har cikin ranta bata jin daɗin wannan katsalandan da Yafendo tayi mata ba. Amman ni kuma kamar in goya yafendo haka naji" Tare suka fice ɗaki ya rage daga ni sai Yaya Hamma. Shi kuma fishi sosai yake yi dani duk fa akan tafiyar tawa ne. Ni sai tafiyar ta fitar mun akai, kuma nayi mishi rantsuwar da ace da kuɗina akayi mun komai da tuni na fasa. Amman yanzu in nace na fasa hajiya Salamatu ba ƙaramin bacin rai zata nuna ba, kuma ƙila ita kanta uwani in ja mata. Yaya Hamma ya jikin naka?" "Da mutuwa ma zanyi kila hankalinki sai yafi kwanciya ko?" Sai naji faɗuwar gaba har idanuna suka kawo ruwa. Cikin rawar murya nace. Ko kusa bazan ji daɗi ba. Kayi haƙuri tafiyar da zanyi ta dole ce, kuma bazan shige shekaru uku ba zan dawo. Kuma ina fatan in dawo in sameka a cikin aminci. Ɗan murmushin gefen baki kawai yayi mun. "To ki shirya tare zamu tafi kanon. Bazan dawo ba har sai jirginku ya tashi. Idanu na zaro nace. Ka rufa mun asiri kar kasa matarka ta bindigeni. Kai da baka da lafiya kuma sai in ɗaura maka wahala? Wallahi ka barshi. Hararata yayi mai cike da tsantsar so. "Ai ratayayyen hakkine a kaina inga tafiyarki." Shiru nayi zuchiyata na doka mun tambura. To Allah ya baka lafiyar Yaya Hamma. Ni zan zo in wuce" Sallama nayi mishi na fito da furata a hannuna a ɗakin Boɗɗo na shanye furata. Washe gari Dada ta kawo mana ziyara da su Cubu dan muyi sallama. Tayi mun nasiha mai ratsa zuchiya sosai. Nayi kuka kamar raina zai fita. A daren na kasa baccin kirki. Ina kwance Daso ta shigo ta tsaya a kaina. "Sai ki tashi Yaya Hamma na kiranki. Jabu wallahi kiji tsoron Allah kinzo kin samu mutum da ƴar matarshi suna soyayyarsu gwanin sha'awa. Amman kinzo kin raba wannan soyayyar da shaƙuwa, kin hana Yaya Hamma ya samu lokacin kan shi balle ita Matarshi ta samu lokacin shi itama" Tashi tsaye nayi ina jujjuya maganganun da Daso ta fesomun. Kai kawai na girgiza tare da cin alwashin sai na jero mata waɗanda suka fi wanda ta faɗa mun zafi. Ficewa nayi na barta da ƙunan zuchiya. A zaune na sameshi yana zane a ƙasa da tsinke. Zama nayi a gefe nace. Barka da zuwa Yaya Hamma. Yaya jikin naka amman?" "Jiki da sauƙi Jabu. Ya shirin tafiya? Nasan dai an gama komai ba tun yau ba. Ke naga zumuɗin tafiya ki barni kike yi" Sai naji duk jikina ya mutu. Shine yake ganin kamar ina zumuɗin in tafi in barshi. Amman har cikin jikina inajin zafin kewarshi tun yanzu, bansan kuma ya abun zai zama in na tafi ba. A ranar dai hirar batai armashi ba jikkunanmu a mace mu kai sallama. Harna taka zan shiga gida ya kira sunana. "Jabu" Cak na tsaya. A hankali na juyo muka zuba ma juna idanu na mintunan da bazan iya faɗar adadinsu ba. Ya kasa ce mun uffan. Fitowar Jatau ce ta katse komai. Bai samu damar faɗa mun abinda yasa ya kirayi sunana ba, Jatau ya tareshi da zantuttuka. Cikin na shige na barsu nan. Ina shiga na harari Daso nace. Gobe zan bar garin. Kinga hakan zai baki damar cusa kan ki a wajen Hamma. Kinga in da rabo sai in dawo in sameki kina goyon ɗanku na biyu ke da shi." Ina faɗin haka ta kalleni tace.."haka kika ce mun Jabu?" Ƙwarai kuwa haka nace. In kin isa ki maye gurbina a zuchiyarshi in zaki iya Ni kin ganni nan tafiyata tafi komai mahimmanci a wajena" Kwafa tayi tace dani. "Zan baki mamaki Jabu, zaki san nima macace wacce Allah ya horema duk abun alfahari kinsan dai na fiki kyau nesa ba kusa ba, in banda ma namiji da gane_gane ko me ya gani a jikinki oho" Ni ban ma sake bi ta kanta ba. Itako sai mita take yi da fillanci. Ina kwance shiru duk kewan yarana ya kamani, dama Baban yaran. Can kuma sai Hamma ya fado mun, da kuma alwashin da Daso taci mun. Da irin wannan tunani bacci yayi awon gaba dani. Asubar fari na yi wanka tsab. Ana fitowa masallaci na suri kayana a jakar leda na fito. Na yi sallama da kowa da kowa. Ana cikin haka Yaya Hamma ma ya shigo. Muna fitowa Boɗɗo da mijinta na isowa suma. Sai da suka rakamu fa har Girai kana suka dawo mu kuma muka shiga cikin gari, Yaya Hamma ya samu a motar Kano. Sassafe motarmu ta hau kwalta. Sai da tafiya tayi nisa Yaya Hamma yace. "Inaso ki mun wani alƙawari Jabu. Nasan kina da riƙon alƙawari na san hakan silar shaƙuwarmu. To ki mun alƙawarin da kika tabbatar zaki cika mun shi. Kar ki yaudareni in yayi miki tsauri ki ce mun ba zaki iyaba" A sanyaye nace dashi. Faɗi alkawarinka a shirye nake da in cika shi. Matsayinka ya wuce hasashenka" Daɗi yaji sosai. "Ki mun alƙawarin ba zaki wuce shekaru ukunnan da kika ɗebarma kanki ba. sannan ki mun alkawarin ba zaki kula samari ba dan Allah. Sannan ki mun alƙawarin ba zaki dawo kiji ke kinfi ƙarfin zama tare damu ba. Bi ma'ana kar ki sake halayyarki, sannan ki mun alƙawarin riƙe mutuncinki" Shiru nayi mishi ina murmushi kaina na ƙasa. "Au ke dariya ma na baki ko? Kin kyauta ai" Ɗago kaina nayi na kalleshi. Yaya Hamma na karɓi duk alƙawarurrukanka. Allah yai riƙo da hannayena in cika maka alkawarurrukanka. Amman ina da taambaya..." "A'a Jabu ".. yayi saurin dakatar dani ta hanyar ɗaga hannayenshi. Ba shiri na yi shiru da bakina. "Ni dai tunda kin ɗaukii dakon alkawarina ai Shikenan. Ni kuma zan yi zaman jiran dawowarki, tare da miki fatan samun nasara kuma" Daga haka kuma mu ka ɓige da hirarraki, ya dinga bani labarai dangane da al'adun Fulani. Ni kuma dama na kasance ma'abociyar son tarihi ce da duk abinda ya shafi gargajiya ta ko wanne ƙabila. Allah cikin ikonshi da amincewarshi muka isa garin Kano. Kai tsaye gidan Uwani muka ya da zango. A gidanta muka ci abinci. Yaya Hamma ya fita zuwa masallaci dan rama sallolinshi, nima na rama nawa sallolin. "Baki ga yanda kuka dace ba wallahi. Ashe kyakkyawane Yaya Hamman naki. Kuma na lura gaskiya yana tsantsar sonki. Munafuka kema fa kin soma sonshi. Ni dai amman bana bayan wannan soyayyar ruga ba wajen zamanki bane" Dariya mu ka yi dukka. Hakane Uwani wallahi na tsunduma cikin sonshi. Shi kuwa dama ba'a magana dan shi ya koya mun yanda zan so shi. Sai dai fa akwai kura Uwani" Sai da ta gama dariyarta tas kana tace mun. "Ƙurar me kuma Iyabo, akwai wata matsalar ne?" Nace da'ita. E to akwai matsala ta ɓangaren matarshi, da ɓangaren yarinyar ƙanwar Dadanmu Daso wacce nake gidansu a zaune. Matsalolin du manya ne daka iya dakile soyayyarmu. Matarshi tunda aka kai mata gulmar ana ganin mijinta a wajena, sai ta tayar da ƙayar baya, kullum cikin fitina dashi take. Ke har shanunshi daya siyar ya bani kuɗin ban karɓaba sai da su kai rikicin da har mahaifiyarshi ce ta shiga. Ƙanwata tana Aure a gidan Uwani tana auren ƙanin shi hamma ɗin. Sai suka tsiri zaman doya da manja. Ita kuma Daso ko tsaiwa da zaurawa bata son yi kwata kwata duk sabida da shi. Akwaifa wani abokin mijinta mai rasuwa da yake tsantsar sonta. Yarinyarnan fur ta dire wai bata sonshi. Ni kumaa a jiya ta caccakamun magana akan wai Hamma na zaman soyayya da matarshi ni nazo shiga tsakani na hana aci soyayyarnan yadda ya dace. To kinsan mu mata, saina caccaka mata nawa maganganun nace ta aurshi in dawo in samu tana goyon ɗansu na biyu. Ita ma cikin fishi sai tace zan gani. To jiya da ƙyar nayi bacci Uwani " Dariya muka dinga yi ni da Uwani. "Ni dai shawarar da zan baki wallahi ki raba kanki da wani auren ruga, kiyi fatali da wani Hamma. Kinga ƙasar zamu bari Iyabo soyayya ba taki bace. Shigowar Yaya Hamma da Hafizu ne ya dakatar da tattaunawar tamu. Sun zauna babu daɗewa nace. Uwani Hafizu mu kam zamu tafi gida. Sai gobe kuma in Allah ya nuna mana." Tare su kai mana rakiya izuwa titi har sai da Bus ɗinmu ta tashi sannan suka juyo. Kwatsam su Iyaa suna tsakar gida suna wannan hira tasu mai kamar faɗa muka shigo. "Ah Ah ah ah Iyabo. Ikabo ( sannu da zuwa)" Nan ta miƙe ta soma rawa harda guntuwar waƙarta su Iyaa Beji na mata dariya. Dukkansu saida na bisu ɗaya bayan ɗaya na dinga zubewa a gabansu ina kwasar gaisuwa bisa ga al'adarmu. Yaya Hamma dai duk abinda yaga nayi shi yake maimaitawa. "Lekan, Lekan woo ah" Lekan ya amsa da karfi sai gashi harda gudu. "Ahh Antimi Iyabo Ikabo o ti dara osale ( Anti Iyabo Sannu da zuwa Ina wuni?)" Owo bawo ni o se n se? ( Yaya kake Lekan)? Nima na tambayeshi da yarenmu. Hannu ya miƙa suka gaisa da Yaya Hamma kana yace mun. "Owo mo dara Antimi ( Ina lafiya Anti) "Mu u lo si yara re ( Kai shi ɗakun ku) Cewar Iyaa. Ni kuma ta jaye hannuna muka shige ciki. "Ashe dai zaki zo Iyabo? Nayi kewarki sosai. Sai inta mafarkin ki. Har sai da Debisi yaje ya dawo ya tabbatar mun kina lafiya sannan na samu nutsuwa. Sai kika ga Debisi ko?" Murmushi nayi mata nace. Sai gashi Iyaa babu zato" Dariya tayi kawai kana tace. "Duk abinda babba ya hango yaro ko ya hau bishiyar rimi ba zai hango ba. Dama dan ya samu nutsuwa ne yasa na ce ya aureki dan zaki fi ganin darajarshi da kimarshi sama da ko wacce mace. Amman sai ya nuna shi baya so. To wacce yake so din gasu can kullum cikin faɗa, ko jiya uwar haka suna gidannan anata shari'ar da ni na gaji da'ita. Yanzu dan Allah da ke ya aura hankalinshi ba kwance ba?" Kasa amsata nayi, dan da kunya Debisi dai ita ta tsugunna ta haifeshi. "Shi wannan ɗin da ya rakoki ko shine oko omo obirin ɗin nawa? (Sirikina). Kai na sauke ƙasa nace. A'a yaron Ƙanwar Dada ne. Dama zan tafi saudiyya aikataune shine ya biyoni in mun tashi sai ya koma shi kuma" "Ah Ah orira ( abun mamaki) Saudiyya fa kika ce?" Sai ta miƙe ta shiga rawa tana jero mun waƙoƙin sanya albarka. Har sai da ta tara mun matan gidan. Nan take kowa yaji abinda ke faruwa. Nan gidan ya kacame da waƙoƙi da murna. Bayan sun tafi ne Iyaa ta bani Amala tace. "Ki kaima Ɗan uwanki amala yaci abincin yarbawa" mayafina nasa na ɗauki kwanon na fice zuwa ɗakin lekan. Da sallama na shiga na samu yana kallon wani film na yarbawa. Shi kaɗaine a ɗakin sai lemun kwalba na limca dake gabanshi. *Ƴar uwa ina fatan baki mance da kayan ƙamshin Mrs Bukhari gidan ƙamshi ba ko? Ƴar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ƙamshi. Matso kusa ƴar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ƙamshi ya riƙe miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake saƙawa a tsakankanin kaya. Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ƙamshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata. Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haɗe da turaren fesawa a gashi. Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ƙara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ƙamshin kifi ɗanye. Inada humrori kala_kala. Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ƙamshi. Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ƙamshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ƴar mutan Maiduguri kin samu ƙamshi. ( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai ɗauke da abubuwa huɗu manya kuma a kan kuɗi ƙalilan karki bari garaɓasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)* [8/8, 3:11 PM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE.... LITTAFI NA BIYU 3 A hankali na isa na zauna a gefenshi. Idanu kawai ya zuba mun sai naga yana kaɗa kai.. Kwanon abincin na tura mishi gabanshi. Ga Amala abincin bugun gaban yarbawa da fatan kana iya ci" Dariya yayi mun yace. "Tun kafin ki zo duniya nake cin Amala. Ai nayi zaman oghomosho, sarkin garin Oghomoshon ma bafulatanine. Kinsan tun shekaru aru aru yarbawa suke a matsayin bayin Fulani. Hakanne yasa auratayya tayi ƙarfi a tsakanin Yarbawa da Fulani. Sai kiga bafulatani sak amman sai kiji bai iya ko fillancin ba sai yarbancin. Haka sai kiga beyerabiya na zagargaza fullanci. Ki duba Dada yanda naga da yarbanci zalla take magana dake." Ajjiyar zuchiya na sauke nayi dariya. Shima dariyar yayi ya soma kantara lomar Amala miyar ewedu sai dalali take yi a hannunshi. Sai da ya cika bakinshi da ( phomo) ganda kana yace. "Ni ko kibar matan yarbawa na birgeni, kuma Allah ya zuba musu sura masha Allah ." Dariya nayi sosai nace. Ku da kuke da farare kuma siraran mata masu gashi" Dariyar shima yake yi mun. "Jabu kenan. Ai cikakkiyar mace ƴar duma_duma daban take da siririya. Shi kyau a sura yake ba'a fuska ba ai. Bance sirara basu da kyau ba. Kuma bance yarbawa sun fi filani kyau bane. So nake ki fahimta, wani namijin mai sha'awar haɗa shinkafa da doya ne. Wani kuma taliya kaɗai ta wadatar dashi" Cikin karantar yanayinshi nace dashi. To kai a wacce matsayar kake ne?" "Koma a wacce nake zaki sani ne" Cikin raha dai mu kaita hirarmu har ya kammala cin abincin nashi. Kana nayi mishi sallama na tafi. Sai zuwa washe gari na haɗu da su Burodami kokodeen da su Burodami Debisi. Kuma na zagaya gidajen nasu naga yaransu, na gaisa da matansu. Yemisi dai babu yabo ba fallasa, dama ya lafiyar kura ballantana tayi hauka. Haka dai akaita mana shirin tafiya, dan har munje anyi mana gwaje_gwaje iri da kala a asibiti. Ana washe gari zamu tafi ko bacci na kasa yi dan dadi, da kuma wata fargaba data lulluɓeni. Burodami Debisi, da Yaya Hamma, da Hafizu sune abokan rakiyar tamu har zuwa filin jirgi, ko ince ɗakin jira. Gefe guda muka keɓe da Yaya Hamma da jikinshi naga har rawa yake yi, idanuna a cike da ruwan hawaye. Naso Yaya Hamma ya furta mun kalmar so kafin in tafi ya jaddadamun matsayina a zuchiyarshi. Amman kunya da ƙauyanci ya danneshi. Haka dole mu kai sallama ba tare da naji inda soyayyarmu ta kwana ba. Ko da muka shiga cikin Bus ɗin da zata kaimu gaban jirgi ai sai na sake fashewa da kuka, ina tunano fuskar Yaya Hamma, da yanda yake ta aukin jaddadamun alƙawarinmu. Burodami Debisi kuwa kamar ya shaƙo Yaya Hamma ya rufeshi da duka haka yake ji. Gurin dake ɗaure a shintsiyar hannunshi daya bani na sake damƙewa a hannuna. Yau ni Iyabo gani a cikin jirgin sama zai tashi damu zuwa ƙasa mai tsarki. . Hukunci sai mai tsaga idanu. Allah sarkin girma in ji kishiyar mai duwawu. Maraɗi Gwadabe:. Auwala bai dire Sabitu a ko ina ba sai a gaban malam, ga almjirai cike da wajen. Tun kafin Malam yayi magana. Baba Asshi ta fito babu ko mayafi a jikinta. Kallon da taga gardawan Malam Magaji na yi mata ne yasa ta koma daga zaure. "Auwala wannan wanne irin riƙo kayi mishi kamar ka kamo barawo" Malam ya girgiza kanshi yana bin ƙofar zauren da kallon baƙin ciki. Baba Fhatsima ce ta fito saye da katon mayafinta ta jaye Hadiza tare da cewa. "Koma me ya faru a barshi a tattauna a cikin gida. Auwala cikashi, kai kuma Sabitu jeka abinka. Allah yayi muku albarka baki ɗaya. Hadiza ta jawo suka shigo zauren Baba Asshi ta harareta sama da ƙasa tace. "Ni nawa yaran sai ki tsine musu ai, tunda naki kika sama albarka. Ni na ji jaraba fa, kun bi kun sani a gaba Fhatsima kin hana mun jin daɗin aure" Baba Fhatsima Taso tsaiwa ko wacce zata hanata bacci ta feso mata. Auwala sai ya kama hannunta suka shige. Su kuma su Gwadabe suka wuce barayinsu dan watsa ruwa su ji daɗin jukkunan nasu. Gwadabe yana wankannan yana tunanin me yasa gida in da mace sama da ɗaya ake yawan samun rabewar kai ne. Ta ina kuma matsalar tafi rinjaye tsakanin matan, ko uba da yake zama majingina a wajen mata da yaran gida.? Da wannan tunanin ya fito. Fitowarshi ke da wuya Ine tazo ta yi kiransu gabaki ɗaya harda Gwadabe izuwa turakar Malam. A babban falonshi duk suka gurfana Malam ya soma magana da cewa. "A wannan karon duk macen data nuna zata kawo mun rabewar kan ƴaƴa ni zan iya sallamarta ta tafi gidansu. Allah yana gani daidayya ina bakin ƙoƙarina dan ganin nayi adalci a tsakanin matana harma da su yaran nawa. Ke Fhatsima kece Babba a gidannan na faɗa ba tun yanzu ba zan haɗe kan yarana da matansu dukka a gida ɗaya dan su rayu tare yaransu su cuɗu da juna ta yadda zasu shaƙu da junansu. Wannan magana tamkar a rubuce take ba fashi. Duk da Asshi ta nuna ita bata bukatar a haɗe yaranta dana Fhatsima. Harma Jamilu ya goyi bayanta a kan hakan. Rikicin Sabitu da Hadiza ne yasa na dawo da wannan maganar baya. Nasan ko wacce nayi mata bayani ita kaɗai Amarya malam uwar kissa ta dubeshi da taushin murya tace. "Allah shi gafarta malam ni nawa yaran da suka kasance ƙananu ya za'ayi dasu to?" Dariya malam yayi cikin so yace. "Amarya harda su Rabi'u za'ayi wannan ginin. Su kuma mata _matan da zasu yi aure ko wacce zan bata kadara a matsayin kyauta, kanana marasa aure kuma sai in ajjiye musu zuwa lokacin da Allah zai ƙadarta su yi aure. In kuma ta Allah ta kasance a kaina sai a danƙa musu baya cikin gado na basu halak malak, hatta ginin da Shi Tasi'u zai musu baya cikin gado na mallakawa kowa halak malak harda Gwadabe dan gudun kar in kwanta dama tashin tashina ta tashi. Dan kuna ganinane kuke samun damar faɗace_faɗacen nan da kuke yi. Wallahi duk ranar da za'a wayi gari bana doron ƙasa zaku yi dana sani, za kuma kusan mahimmancina. Zaku iya tafiya" A lokacin dai jikkunansu duk ya mutu, amman kowacce tana jaye ƴaƴanta suka shige ƙurya sai labari yasha banban. Wannan kyauta da malam ya furta bata cikin gado itace ta tayar da ƙayar baya, baƙin ciki da hassada ya shigo, musamman ga wadanda basu da damar cin tudu biyu. Haka bikin yaran gidan yaci gaba da matsowa, sai shirye_shirye aketa ta faman yi kowa ta ciki na cikinta. Yaya Tasi'u da matarshi Anty Badi'at ba zama, dan ita ta shiga cikin nijer ta siyo kayan gadajen Amare da kayan kitchen ita da Amaryar Malam. Kwana bakwai da Baba Magaji ya ba Gwadabe ta cika, Baba Magaji baice komai ba, shima Gwadabe yaƙi cewa komai, zuchiyarshi kullum cikin taraddadi take kawai, har aka tsunduma sha'anin biki dai Baba Magaji na kallon Gwadabe ya zuba mishi idanu. To al'adar auren Maradi ya banbanta da al'adar aure a Najeriya ƙasar hausa. Su yanda suke bikinsu shine. *KAN GORO* Shi yanda ake yinshi shine. Iyayen Ango zasu tawo da goronsu a jarka za'a daddaleshi, yana danganta da yanayin karfin miji. Zasu tawo da balis ( Akwati) wasu suna zuba kaya a ciki, wasu kuma basa zubawa, zasu tawo da kuɗin sadaki, da hidimar girke_girke rigi_rigi. Iyayen Amarya maza su kuma zasu zauna a manyan taburmai domin tarbar iyayen ango da wannan kaya. Iyaye mata a gida kuma zasu yi girki na alfarma a fito dashi. Anan za'a tsayar da lokacin Aure da bai haura wata guda ba, wasu ma sati guda ya danganta. To su dangin Ango zasu tafi da wannan gara ta dafaffen abinci tare da tsayayyen lokacin Aure. *LIFARAN* shi kuma lifaran ( Anko) ake nufi. Daga kawo wannan kayan aure da kuɗi. Dangin Ango, da dangin Amarya sai su fidda Ankon biki. *LALLE* Amarya zasu zauna zaman lalle na kwana biyu ita da ƙawayenta. *KUƊIN SIGA* Shi kuma kuɗin siga kuɗine da dangin Amarya suke hidima dashi ma dangin ango. Akwai kuɗi uwa ko kuma ai mata kaya, da su saitin bahuna, da turmin zani na goyo. Shi wannan setin bahunan da turmin zani ana bayarwane a matsayin an mayarma da uwa zanin goyo da bahunan wankan Ango lokacin da yake jariri, da sontolon tsaba duk na uwar miji. Sai buhunhuna hatsi na gara bana wasa ba. Hatta facala in amarya na da shi akwai kudinta, kudin abokan ango na zirga_zirgar biki, sai buta da Dadduma, da jikka biyu na kudi na uban miji. Baki ƴan nesa kuma da suka tawo biki, ana zuba tsaba a roba da turamen zannuwa a basu. Su kuma sai su ba da jikka goma na uwar Amarya a matsayin tukuicin wannan hidima ƊAURIN AURE. Su kuma da safe akeyin ɗauri in dai na budurwane. Sannan ana fitarma da maza ƴan ɗaurin aure abinci waje aci asha a goge wuya. *WATSI* Wannan ɓangaren gidan ango ke yi. Bayan isha ko bayan magriba za'a shinfiɗa tabarma a zaunar da ango a tsakiya. Ai ta mishi watsin cingom da kudi shima ya danganta da ƙarfin dangin ango, amman a wannan watsin ango na samun kudi ainun. ƊAUKO AMARYA Bayan an gama watsi kuma dangin Ango zasu je su ɗauko Amarya a kaita ɗakin mijinta. Iyaye suna yin hidimar kayan ɗaki sosai, gado biyu suke yi, banda kafet_kafet da manyan daddumai. *YININ BIKI* Shima bikine rigi_rigi ake yinshi, sannan a yinin bikinnan suke sa anko dangin ango dana Amarya. Ayi yinin biki a watse shikenan biki kuma ya ƙare. Daga cikin wannan sha'ani na biki babu wanda aka raga. A zahirin gaskiya an kashe kuɗaɗe sosai, duk wata hidima da akayi Tasi'u da matarshi ce suka gudanar da duk wani kashe kuɗi. Gwadabe kuma a lokacin sha'anin bikinne ya karema ragowar ƴan matan gidan kallo tsab. A tsahirance sunfi Hadiza kyau ta fuskokinsu, sai dai ita kuma Hadiza ta fisu diri da kiba, dan shi kuma baya sha'awar mata sirara sam. Da wannan dalili nashi ne ya ƙudurce a ranshi da zaran an watse biiki zai tunkari Baba Magaji da batun Amincewarshi ga Hadiza. Ga Tamu ko da yaushe su kai waya yakan yi mishi tuni da batun ƙanwarshi da take zaman jiran Gwadaben. Harma sun yi waya sau biyu haka. Yanda ya ɗan taɓa hira da'ita sai yaji babu dai wata matsala a tattare da'ita ko na rashin tarbiyya, ko na fitsara irin ta wasu matan. Ƙarshen wayarshi da Tamu a cikin hidimar bikinnan yake cewa da Gwadabe. "Gwadabe duk ɗan abinda ka rarumo na kudin moya kazo ayi aurennan kowa ya huta. Bara'u yace ya ɗauke maka sadaki. Ni kuma zanyi mata akwati da kaina. Aure kawai zaka zo a ɗaura, sabida manema sun soma damunta, duk da dai bata ƙarashe karatun ba amman ƙiris ya rage' Jin wannan batu ne yasa Gwadabe kiran Bara'u yai mishi bayanin halin da yake ciki akan ɗiya da Baba Magaji ya bashi harma da kyautar wajen zama. Bara'u shi kuma ya tafi kafa da ƙafa har Habuja su kai magana da Tamu. Ya nuna ai wannan ba komai bane, Gwadabe mijin mace huɗu ne bama biyu ba. A take suka kirashi suka tsaida magana kan da zaran yarinyar ta gama karatunta za'ayi auren. Ƴan biyu dake hannun Tamu sai wayau suke yi, suna karatunsu hankali kwance. Ayashe tana riƙe dasu da amana ta game yaran da nata ta maishesu tamkar yaran data tsugunna ta haifa. Haka ma Toye yana zuwa makarantar boko data allo, suna zuwa gona yin noma. Dan Bara'u ya siya musu ƴar ƙaramar gona da yaron wajenshi, harma bana sun noma gyaɗa na kwano uku, da taimakon Sakina dake rakasu gona tana kuyi wannan ku bar wancan Amare sun tare a gidajen mazajensu lafiya, hankalin iyaye ya dawo jikinsu kuma kowa ya ci gaba da sha'anin gabanshi. Wata ranar talata da daddare bayan su Gwadabe sun gama karatun dare sai ya nemi ganawa da Baba Magaji kan batun Hadiza. Dan yaga tun bayan da aka yi bikin gidan. Sai zawarawa suka shiga zurubtu akanta, suka shiga hidimar kashe mata kudi. Dan samarin nijar jaruman gaske ne akan matansu. "Baba Magaji dama akan maganarmu ne da kai. Shine nace na zaɓi Hadiza kamar yadda kaima ka zaɓa mun tun farko. Sai dai akwai ƙanwar abokina Tamu da shi Tamun ya bani tun kafin in tawo nan ɗin. Shine nake tunanin in ka amince sai a haɗa tare ayi bikin lokaci guda. Tunda ita yarinyar kafin lokacin da aka kintata na bikin zata kammala karatun da take yi." Ƙur Baba Magaji yayi yana kallonshi ya jima baice komai ba yanata jujjuya maganar Gwadabe a kanshi. Yana kuma hango irin gagarumar matsalar da ka iya bullowa. Wanda ada ita ya guda, sai gashi ta kuma biyoshi. Bayan dogon nazari da Baba Magaji yayi sai yace. "To Gwadabe naji duk bayaninka. Kuma na gode da nuna sonka da auren Hadiza. Wani hanzari ba gudu ba Gwadabe. Hadiza macace mai ɗan banzan kishi ainun. Kaga kishi? Shi ya hallaka igiyoyin aurenta na baya. Abinda yasa na soka da Hadiza, yarinyace mai biyayya batta da kishi dai. Nayi tunanin kuma ba lallai ka rakito wani auren nan kusa ba, duba da sana'ar taka ma da kake yi har yanzu baka da ido akanta. Kila ko da zaka yi auren sai nan gaba, kila a lokacin Hadiza ta zama babbar mace ka samu sassauci. Kaga mahaifiyarta ko? A lokacin dana auro Asshi sai da muka shafe tsawon shekaru biyu da rabi bata haɗa shinfiɗa dani ba. Kai ƙafarta bata sake taka turakata ba, har sai da santa yaimun lahanin da ya kusan rabani da rayuwata kafin. Gwadabe ina son Fhatsima fiye da yadda kake tunani, kuma ina matukar girmama duk lamarinta. Bata taɓa yin hayaniya ko musu dani ba. Shawarar da zan baka shine. Kaje ka auri ƙanwar Tamu ɗin, ita kuma Hadiza Allah ya fito mata da wani mijin. Gudun kar zumunci ya taɓu dukkanku ƴaƴanane. Tashi kaje Allah yai maka albarka". Gwadabe yaso Baba Magaji ya bashi dama yace ko da wani abune. Amman sai ya ki bashi wannan damar haka dole ya tashi ya tafi. Kuma tsakani da Allah Hadiza ta kwanta mishi fiye da yanda ƙanwar Tamu ta kwanta mishi. Dukkansu a cikinsu baiga na ajjiyewa ba, abu suka haɗe mishi goma da ashirin, ga tunanin Iyabo wanda yake ɗamfare a zuchiyarshi babu dare bare rana. Da Hadiza yaci karo a zaure zata fita taci kwalliya da bakar lafaya ta zubo gashinta gaba. Murmushi ta sakar mishi da ganinshi. Shima yai mata murmushin tare da cewa. "Sai ina da wannan kwalliyar kamar zaki gasar sarauniyar kyau?" Dariya kalaminshi suka bata, sai da ta dara kana tace. "Sallama akeyi dani a waje Yaya. Bansan ma ko waye ba" Sai yaji nan nake kishi ya lulluɓeshi dan ai Gwadabe gwanine na ƴan kishi mun sani tun a baya. Ƙin magana yayi da yaga tana shirin wuceshi ne yace. "Ke daga an aiko ana kiranki sai ki fito harda caɓa kwalliya haka? To maza ki koma Baba batai miki bayanin suna son haɗamu aure bane, ko ni dinne bakya so talaka?" A zabure ta ɗago ta kalleshi cikin maɗaukakin mamaki. Shi kuma yai tsai yana karantarta. A madadin yaga damuwa sai yaga akasin hakan. Dan bata san sanda ta kwashe da dariya ba, ta juya ta shige gida da sauri halamar dai itama fa tana ra'ayinshi yayi mata. Kanshi ya dafe tare da jin haushin kanshi kan furta wannan kalma mai nauyi. Tsoronshi Allah, tsoronshi kar sanadiyyar aurensu zumunci ya taɓu. Dan ƙasan zuchiyarshi gurbin son iyabo ne, tsakiyar zuchiyarshi kuma na ƴaƴanta ne. Ko wacce irin macece zata rayu dashi sai dai ta rayu dashi a saman zuchiyarshi. Yana tsoron rashin adalci, yana tsoron fitinar mata biyu da rabe_raben kan ƴaƴa irin na gidan Baba Magaji. To wacece ta cancanta Gwadabe ya aura a cikin mata biyunnan? Wani shashe na zuchiyarshi yace. "Ka ba ko wacce daga ciki lokaci ta fayyace maka irin sonta, a ciki sai ka zabi guda, guda kuma ka bata haƙuri. Cikin rashin tunanin abinda hakan ka iya haifarma ɗaya daga cikin matar da za'a ba hakuri Gwadabe yai na'am da shawarar zuchiyarshi ba tare da yayi hangen nesa ba. Wannan shi ake kira nama ya dahu romo ɗanye. Nan Gwadabe ya raba lokacin shi ta hanyar rabashi a tsakanin Hadiza, da Shafa, Hadiza suna keɓewa suyi zance, yayin da Shafa kuma yake kiran wayarta su sha hira. Yana auna kalaman ko wacce a zuchiyarshi, yana nazari dan gano wacce tafi sonshi da nuna tausayinshi. Tun Baba Magaji bai san Gwadabe na zance da Hadiza ba har mata suka tsegunta mishi. Kuma Baba Fhatsima, da yaya Tasi'u, harma da su Auwala sun aminta da wannan haɗin kuma sun yi farin ciki sosai. Baba Magaji ranar yaso su tattauna da Baba Fhatsima akan batun Hadizan da Gwadabe, kasancewar ranar ita ke da miji. "Fhatsima naga kamar Hadiza ta amince da soyayyar Gwadabe ko?" Ya jefo mata tambayar yana daga kwance, ita kuma tana kasa a zaune tana dama mishi furar da duk daren duniya sai ya sha kafin ya kwanta. " Kwarai ko. Nima kuma na daɗa ƙarfafarta naga Gwadabe yana da hankali." Kai Baba Magaji ya gyaɗa yace. "Hmm Hadiza kenan. To abinda ta guda a gidan uban yaranta shine ya sake biyota. Kishiya ba? Dan abokin Gwadabe Tamu ya riga ni ba Gwadabe ƙaunarshi, kuma ya riga ya karɓa tun kafin yazoshi. Ni da naso dakatar dashi neman Hadiza dan harna sanar dashi dalilin mutuwar aurenta na baya. Amman bamu san me Allah yake son nunawa ba akan hakan, ƙila wata ayar zai saukarma mata masu kaso aurensu sabida kishiya. Allah ya daidaita tsakaninsu" Shiru Baba Fhatsima tayi kawai. Furar da take damawa ta dakatar da damata. Lokaci guda ta jagule. Hakan yai sababin sawa Baba Magaji ya mike zaune ya sakko ƙasa daf da'ita. Yayi ƙasa da muryarshi yace. "Fhatsima kiyi haƙuri a bisa kalamina. Allah ya sani ba dake nake yi ba, da ita Hadiza nake yi. Amman kiyi haƙuri" "Hmm Malam kenan. Ashe nuna kishi ga abinda kake so matsalane a wajen maza mu bamu sani ba? Tunda nake kishina a gidannan tsawon shekaru fin talatin ka taɓa kamani ina shirka, ko na taɓa tayar maka da hankali ne? Ai ko Hadiza batai kishi na hauka a gidan mijinta ba. Allah yayi ƙarewar aurenne dan ku maza in kuka auro wata macen kukan juyama wata baya na wani lokaci kafin ku gama shan romonta. Abunda Hadiza bata da ilimi akai kenan shi yasa aurenta ya mutu a wannan gaɓar. Amman Nagode da wannan furuci naka" Ta ƙarashe maganar tana shessheƙar kuka mikewa tsaye tayi tana shirin barin ɗakin. Malam yayi carab ya cafe hannunta. Tayi sauri ta runtse idanunta tare da fashewa da wani irin kuka mai ɗaci. A wannan daren Baba Magaji ya sha rarrashi da ban baki. Dan har kuɗi ya debo da baisan iyakarshi ba ya bata da safe kafin ta koma ɓarayinta. A haka soyayyar Gwadabe da ƴan matanshi biyu taci gaba da kasancewa. Ko wacce cikinsu na ƙoƙarin ganin ta nuna bajintarta. Danma ba wacce ta san da zaman ƴar uwarta, iyaye sun bar zancan a tsakaninsu. Domin shi Baba Magaji a ganinshi Gwadabe ai bazai haɗe mata biyu a lokacin guda ya aura ba, dole da ɗaya za'a soma. Ta ɓangaren neman Gwadabe kuwa, Allah yasanya mishi albarka a harkar neman. Dan yana da ido sosai na ganin zinariya. A zuwanshi har ya samu zinariya sau biyu, kuma ba laifi madaidaita ne. Hakanne ya bashi damar yi ma Babala aike, ita da Bara'u abokinshi na amana. Da yamma lis yau su Gwadabe suka shigo gidan, sun shawo gajiya sosai. Harda ƴar ledar kayan kwalliya a hannun Gwadabe. Ɓarayinsu suka wuce dai kamar kullum, sai da su kai wanka suka sake kayan jikinsu. Yayi daidai da lokacin Sallah sai suka wuce kofar gida dan gabatar da sallah. Ta ɓangaren Hadiza kuma tayi kwalliyarta me ƙayatarwa sai ƙamshi take faman zabgawa, ga abinci ta ajjiye da kwanukan zubawa, shigowar su Gwadabe kawai take jira. Baba Fhatsima kuma tana zaune daga gefe tana jin wani shiri da ake gabatarwa a gidan rediyo hankalinta yana wajen shirin. Amman idanunta na kan Hadiza wacce tun ɗazu sai gyare_gyaren gashin kanta data bazoshi ya sauka kafaɗarta take yi. Irin wannan ganɗoki ko a aurenta na fari ma bata yishi ba, duk da shima wancan auren Malam ne ya haɗashi almajirinshi ne mijin. "Hadiza sai nake ganin kamar kin zafafa soyayyar da kike ma Gwadabe. Kibi a hankali kinsan halin maza da karya ma mace zuchiya. Ƙila ma bake kaɗai bace a ranshi" Ƙur ta zuba mata idanu tana karantar yanayinta, dama ta soko zancanne taji irin amsar da zata bata. Dan tana son auna kishinta da Malam yake ta ikirarin ita ta biyo" Ƙasa tayi da kanta, lokaci guda sai ta jagule har idanunta ya kawo ruwan hawaye. "Baba abinda ya faru a baya kuskurene wanda bana mafarkin ya sake faruwa dani a gaba. Nasan an yi mun laifi, amman nima na nuna rashin hakurina ƙarara. Wallahi a lokacin da Tsalha ya dinga nuna mun ni ba cikakkiyar mace bace, sai da yayi amarya ya gane kanshi. Banyi tunanin a daren zan rayu ba, wani abune yake dannemun harshena izuwa moƙoshina. Baba ina da kishi mai yawa, anata cewa wai ke na biyo. Ni kuma in sha Allah zanyi koyi da salon kishinki, da dabarun kissarki ta hanyar gina babban matsayi a zuchiyar Gwadabe. Ta yadda ko mata ɗari zai auro bai isa ya haɗemu a matsayin abu guda ba" Kuka ta fashe dashi mai ciwo. MRS BUKHARI Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Jfn7qq4nyMm0prVhnhfVZK *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* [8/8, 3:11 PM] +234 803 969 6400: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Jfn7qq4nyMm0prVhnhfVZK *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE LITTAFI NA BIYU 4 Baba Fhatsima ta dubeta a tsanake tace. "Shikenan ni da kaina zan kwatanta miki yada zaki zauna daram ki wuce wulaƙanci a zuchiyar ɗa namiji. Hadiza a lokacin da Malam yace zai ƙaro aure sai da na kwanta jinya. Amman sabida kirsa irin tamu ta mata ni na haɗa akwatin da Malam ya kaima Asshi. Kuɗin dana samu a hannun malam bana wasa bane. Zuchiya kullum ciwo da zafi suke yi mun Hadiza. Wallahi inna kalli Malam sai inji kamar in ɗura mishi zagi. Amman wallahi ko ɓacin rai baya iya ganewa a fuskata. Horon da nayi mishi na ƙauracema shinfiɗarshine, tunda ya raina iyawata, sai da nasa da kanshi ya gane mahimmancina da kuma banbancina. Duk da ina fishi dashi, saina dukufa shan magunguna ingantattu, musamman tukuɗi da gumbar matan Kanuri da tsuminsu, da shayin su na musamman. Na dinga gyaran kaina dan sake kankaro mutuncin kaina. Ni kishina bana ayi zagi ko bankaura bane. Da duk tsufana Malam har gobe yana mararina Hadiza. Sallamar su Gwadabe ce ta katse wannan tattaunawa wanda nasan ba Hadiza kaɗai ke karuwa da'ita ba, harda masu karatu. Saurin share hawayenta tayi, wanda karab a idanun Gwadabe. "Baba yinwa" Cewar Auwala wanda baya jurar yinwa. Dariya duk aka saka mishi. Baba Fhatsima tace. "Ai kai wacce zata aureka ba zaka barta ta huta da ɗaura sanwa ba" Saida ya cusa tuwo loma babba a bakinshi, tun kafin Mammada ya gama zuba musu, kana yace. "Tabb ai ni tun da jimawa tasan Yaya nake. Kullum naje saita kawo mun shayi da cukui, wataran harda abinci fa." Mammada yace. "Bayan uban abincin da kake take cikinka dashi kafin ka tafi? Shi yasa cikinka kullum yake ƙara girma. Baba yau daya zarme rijiyar haƙon zinariya da ƙyar aka zaroshi tsabar ƙiba fa" Duka Auwala ya kai mishi, yai maza ya matsa kusa da Gwadabe wanda shi kuma hankalinshi na kan gimbiya Hadiza da yaga tana cikin rashin walwala. Baba Fhatsima tayi Dariya tace. "Duk ai ya kusa karewa gini kam gobe za'a soma an kawo bulo da yashi, an yi ginshiƙi. Aikin ba wani daɗewa zaiyi ba tunda an riga da an tanaji kudin aikin. Duk kuyi aurenku nima na huta" Gwadabe yace. "Ai Baba kila fa Auwala ya dinga zamowa cin abinci ɗakinki, baya zage ya kwashi girki a gaban Amarya haka ba" haka dai sukaita raha a tsakaninsu kamar yadda suka saba a koda yaushe. Ana cikin haka Yaya Tasi'u shima ya shigo akayi hirar dashi. Kiran sallar isha ne ya fasa taron. Da Gwadabe ya tashi fita sai ya ajjiye ledar kayan kwalliyar da ya siyo ma Hadiza a gefen ƙafarta ya fita. "Tashi kiyi Sallah kafin Gwadabe ya kiraki zance, dan zancanku ba ɗaga ƙafa. Yaran zamani kome kuke cewa in kunje wajen zancen oho. Zance ai sai su Ine yanzu dai duk ya ƙare." Hadiza tayi murmushi tace. "Gobe ma mu kayi da Anty Badi'a zamu je gidajensu mu ganosu, tun bayan biki mu ta ɓangarenmu babu wanda yaje. Shekaran jiya Sauma'iyya suka je gidan Hafsatu." "Daga gidan mijinta taje, ke yaya akayi kika san taje? Tsegumi" Dariya Hadiza tayi tace. "Baba asshi ce naji tana faɗama Amaryar Malam. Wai Hafsatu ta aiko mata da kuɗi harda soyayyun zabbi" Harara Baba Fhatsima ta doka ma Hadiza ba shiri ta tada kabbarar sallah. Dan babu abinda Baba Fhatsima ta tsana irin gutsiri tsoma" Hadiza tana kan sallayar bata tashi ba Gwadabe ya aiki yaron Amaryar Malam yayi kiranta. Sai da ta kuma gyare_gyaren kwalliyarta kafin ta fita. Baba Fhatsima tana jimantama Hadiza ranar da zata ji labarin bada ita kaɗai Gwadabe yake soyayya ba, kuma akwai yiwuwar ba ma ita kaɗai zai aura ba. Ko da ba'a hade bikin ba, tasan babu wani nisa a tsakani. Fitowa tayi tsakar gidan tana busa ƙamshi. Amaryar Malam da taci kwalliyarta na zuwa turaka ta bushe da dariya, dama can basa shiri sam da Hadiza. Dan bama su wuce sa'anni ba. Ko kallonsu batayi ba. Harfa ta sha kwanar ɓarayin su Gwadabe ta jiyo Baba Asshi na cewa da Suwaiba. "Sabida tsabar tayi bandarine fa Malam ya tafi ya ɗauko ɗan ƙanwarshi dan ya haɗasu. Ƙanwar tashi ma da bata da mutunci. Ni dai na gode Allah in Fhatsima ta fini da soyayyar miji, da ɗa mai arziki. Bata fini a surukai ba. Dan masu arzikin gaske ƴaƴana suke aure. Itako Hadiza gidan da za'a sakata ubanta nema ya bayar" karab a kunnen Hadiza, karab kuma a kunnen Baba Fhatsima. Dukkansu kai suka girgiza kawai. Hadiza tayi shigewarta ciki. A bakin dakalin ƙofar ɗakinsu yake zaune. Ga hasken lantarki tanwar ya haske ko'ina. Gardawan malam su biyar suna wajen suna wankin suturunsu, sai Sabitu dake tsaye a ƙofar ɗakinsu kawai dan babu dai Abinda yake yi. Kwana biyunanne ya tsiri yin hakan a daidai lokacin da Gwadabe zai fito ya zauna domun ganawa da Hadiza. Tun daga nesa Gwadabe yake ƙarema Hadiza kallo. Zani daya gani ɗaure a jikinta sai yake ganin kamar iyabo ce ke tawowa, dan Iyabo ta ƙware wajen iya ɗaurin zani sosai, takanyi matuƙar kyau da zani, ƙibarta na daga cikin abinda ke sa ruhinshi ke fisgarshi akan son Iyabo. Isowar Hadiza ce tasa ya dawo hayyacinshi. Zama tayi gefenshi sosai. "Barkanka da wannan lokacin angon Hadiza mujin mace ɗaya tilo." Murmushi yayi mata kawai, a kullum in ta kirashi da mijin mace ɗaya tilo sai yaji faɗuwar gaba, haka ƙanwar tamu take yawan ce mishi. "Mijina ni ni kaɗai. Babu wata mace data isa ta rabeka" Da sunyi mishi irin furucinnan sai yaji hankalinshi ya tashi a madadin ya samu nutsuwar kalaminsu. Anya bai cutar da zukatan ƴan matan ba kuwa, lokaci baiyi da zai bayyana musu gaskiya ba kuwa? To wai in ya zayyana musu gaskiya du suka gujeshi ya zaiyi da kunyar waɗanda yake ganin darajarsu a jikin ƴan matan? In kuma suka ritsashi suka ce sai dai ya zaɓi ɗaya, Yaya wacce aka ce tayi haƙuri zata yi? Haƙiƙa yayi kuskure mafi girma da rinjaye, awannan tunanin kamata yayi tun farko zaiyi shi, ba yanzu da wankin hula ya riga ya kaishi dare ba." "Wai tunanin me kake yi ne Yaya tun ɗazu inata magana fa, bakace komai ba" Ya tsinkayi shagwaɓaɓɓiyar Muryar Hadiza, wanda tasa saida tsigar jikinshi ta tashi, dan wannan yana daga cikin sabon salon da take son fitowa dashi dan mallakar zuchiyar Gwadabe. "Akwai muhimmiyar maganar da nake son mu yi ni dake. Hadiza banaso ki fassarani da ko wacce iriyar mummunar fassara, ina cikin tsaka mai wuyar fita ne, abinda yasa abinda ya faru ya farun kenan." Shiru tayi tana kallonshi da ƙananun idanunta waɗanda gashi sukaima rumfa. Bayan ta ja numfashi na daƙiƙa sai tace. "Ina saurarenka, zanyi maka shari'ar gaskiya da gaskiya. Faɗamun matsalar dan tuni fuskarka ta nuna matsala zaka faɗa mun" Shiru yayi yana shafan sumarshi kanshi. "Hadiza ba da ke kaɗai nake soyayya ba. Akwai ƙanwar abokina Tamu da ya bani tun kafin in tawo Nijer " Darara dam_dam_dam gabanta yai mummunan tsinkewar daya tunkudo ruwan hawaye nan take suka soma shatata a idanunta. Duk da haka tace. "Dan Allah kace dani wasane, kar kayi amfani da kishin da akace maka shi yai sanadiyyar mutuwan aurena ya zamema logo. Na roƙeka karka yaudari zuchiyar data saba da rayuwa da sonka." Take hankalin Gwadabe ya kai ƙololuwar tashi, dan bai taɓa tunanin Hadiza zata ɗauki wannan lamarin a yanda ta ɗauka yanzu ba. Da ƙyar ya samu kuzarin ce Mata. "Wallahi da gaske nake yi Hadiza. Kafin in tawo nan na riga dana amshi soyayyarta. To kuma da nazo nan sai Baba Magaji yace in zaɓi mace a cikin ƴaƴanshi in aura, amman sai yace yafi mun sha'awarki" "Kenan ba sona kake yi ba, Malam kai ma biyayya? Shikenan ni na hakura kaje ka aureta" Tana gama faɗar haka ta mike fu ta bar barayin. Yayi yinƙurin tareta sai Auwala da shigowarshi barayin kenan ta gefenshi ma Hadiza ta raba ya dakatar da Gwadabe bisa dole ya tsaya." "Koma me ya haɗaku kyaleta ta huce, su mata a cikin irin wannan halin baka iyawa dasu sam." Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke tare da lumshe idanunshi. "Auwala laifi nayi mata. Tana da dalilin yin fishi dani. Laifinane, dan Allah ka bita ka bata baki a madadina" "To wannan ma dabarace. Kai jeka bari in shawo maka kanta ka koma ciki ka jirani." Gwadabe na shiga ɗaki kiran Shafa na shigowa wayarshi. Jiki a mace ya ɗaga wayar, itama yayi mata duk bayanin da yaima Hadiza. Ƙit ta kashe wayarta, ko da ya kuma kira sai yaji a kashe ma wayar baki ɗaya. Dafe kanshi yayi bakinshi na ɗaci, damuwa duk ta haɗu ta dameshi. Hadiza. Da sauri ta shiga ɗakinsu har tana cin karo da Ine wacce suke shirin fita ita da mijinta sun kawo ma Baba Fhatsima ziyara irin ta godiya da angwaye suke yi. Ganin mijin ƙanwarta yasa tai saurin share hawayen dake bin gefen fuskarta. "Ango ka sha ƙamshi kune a tafe da daddarennan? Mu da muke shirin kawo muku ziyara" A ladabce ya gaishe da Hadiza yana yi yana sosa kanshi. "In kin gama kya same ni a waje ni kam" Yace da Ine wanda hankalinta yake kan Hadiza. "Yaya Hadiza nifa fishi nake yi wallahi. Tunda kuka kaini ba wanda ya sake leƙoni ma" Ta faɗa a karaye yayinda Hadiza take kallonta da halamar tuhuma. Ganin hawaye na neman ɓallewa a idanun ƙanwar tata ne ya tabbbatar mata tana cikin damuwa, ko kuma kewar gida." "Ki sha kuruminki dama gobe zamu je gidanki ni da Anty Badi'a. Yanzu dai kije ki samu mijinki karki barshi yaita jira" Ine tace. "Bamu shiga cikin gidanba ma, yanzu dai zamu zazzagaya, amman munje ɓarayin su Yaya Tasi'u." Fitarta shigowar Auwala yana kwaɗama Hadiza dake shirin zama kira. Shigowa yayi ranshi a matuƙar ɓace. "Ke meye ya haɗaki da Gwadabe, da har yake kiranki kina ƙin tsaiwa? Ki sani wanki ne Gwadabe, kuma mahaifiyarshi ƙauna take ga Malam." Hadiza najin wannan sababi na Auwala sai ta saki rushin kuka tana faɗin "Ni wallahi na fasa auren. Yaje can ya auri ƙanwar abokinshi. Ai ba sona yake yi ba. Malam ne ya cusani wajenshi" Duka Auwala ya kawo mata. Baba Fhatsima dake zaune tana kallonsu tace. "Bita a hankali Auwala. Zo zauna inji meke faruwa haka uhm?" Zama Auwala yayi a ƙasa, yana dokama Hafiza harara. "Ki buɗe baki kiyi mun bayani Hadiza. Menene ya haɗaki da yaiyen naki?" Hadiza ta kwashe yanda Gwadabe ya faɗa mata ta sanar ma Baba Fhatsima. Tsaki dogo Auwala ya ja yace. "Ni nama ɗauka wani muhimmin abune yanda naga Gwadabe duk ya damu. To sai me dan ba da ke kaɗai yake soyayya ba, dama cewa akayi dan ke aka halicci Gwadabe ke ke kaɗai? Baba kinji fa abinda take cewa, wannan baƙin kishin nata ne yasa ta tsallake yaranta ta dawo gida. Tana da aiki ja matsawar irin wannan ƙazamin kishin bai fita a ranta ba." Shiru Baba Fhatsima tayi, tana sauraren ɓaɓatun Auwala, da sautin kukan Hadiza. Ajjiyar zuchiya ta sauke kana tace. "Hadiza kina nufin ba zaki taɓa zama da kishiya ba ko me kike nufi? Bar ganin ina goyon bayanki Hadiza, ai in dai wai ke bazaki zauna da kishiya bane, to ya fiye miki sauƙi ki ƙare rayuwarki a gidan mahaifinki. Dani da Malam mun san bake kaɗai Gwadabe yake nema ba, kuma a haka muka ji yafi miki ki aureshi. Dan Gwadabe yarone mai hankali da kunya. Ke dai kiyi fatan kasancewa uwar gida a gidanshi kawai. Kai Auwala tashi yi tafiyarka, ka kuma cema Gwadabe ya kwantar da hankalinshi Hadiza mu muka bashi ita, duk duniya in banda ƙaddara babu wanda ya isa soke batun aurennan. " Tashi Auwala yayi ya dubi Hadiza yace. "Yara basu ajjiye komai ba sai sakarci. Ni zan so ma Malam ya soma aura mishi waccan ɗin kafin ita. Gashi ita ƴar birni wayayya da'ita, kuma hankalinshi take janyewa sosai. Maza ki tsaya kallon ruwa kwaɗo yayi miki ƙafa" Baba Fhatsima ta daki ƙafafun Auwala dake son tunzura Hadiza. "Ja'irin yaro, fice ka bamu waje" Ta faɗa cikin sigar wasa, fita yayi yana sake kambaba yanda budurwar Gwadabe take kulawa dashi a waya. Kuma duk dan ya tunzura zuchiyar Hadiza ne. Ai kuwa yaci nasara dan take zazzaɓi me zafi ya luluɓeta, sai hawaye idanunta yake fitarwa" Harara Baba Fhatsima ta doka mata tare da cewa. "Shashasha maza dai ya gane kishi shine logonki kiga in baki faɗi ƙasa warwas ba. Ba'a ƙarin aure ni Malam yayi mun har kishiyoyi uku? Da banyi haƙuri ba ke kina ganin zan kai haka ne? Ai mace a gidan aure da jarumta akeson ganinta Hadiza. Dan Gwadabe ba ke kaɗai yake nema ba, ba hujja bace na cewa ke kin fasa aurenshi ba. Ai kina gani a cikin gidannan dama dariya suke yi ta mana. Ko baki ji Abinda suke cewa bane ɗazu da zaki je wajen Gwadaben? Ai kinji sarai. Maza dai ki ma kan ki shaidar da babu me iya goge miki ita na zafin kishi. Ni kinga tafiyata Malam na son ganinmu dukka a turakarshi, Allah dai yasa lafiya. Dan malam bai fiye haɗe kan matanshi ya tattauna dasu baki ɗaya ba, yafi gane ya tattauna da kowacce ranar girkinta" Tana gama faɗar haka ta sa kai ta fice ta bar Hadiza da jinyar zuchiya. Yayinda maganganun Auwala suka shiga yi mata amsa kuuwa. "Ni inata wahalar da kaina na son ganin na burgeshi. Sai gashi ashe wata a waya kawai take jaye mai hankalinshi. Ni Hadiza zan iya zaman kishi a karo na biyu kuwa? Wallahi nasan mata ƴan uwana da yawa ba zasui mun uziri ba Wasu ma zagina zasu yi. Amman Ubangijin da yayi ni, ya yiku. Shi ya banbanta zuchiyiyoyinmu. Wata abinda tata zuchiyar ta ɗauke, wata in akace sai zuchiyarta ta ɗauke wallahi mutuwa za tayi. Ni Hadiza macece mai mugun kishi mai zafi, nifa ko baiwace na fi son ace tawace ni kaɗai babu mai irinta. Kishi ni shine raunina nasan ko wacce mace da irin rauninta." Baba Fhatsima" Lallai hausawa sun yi gaskiya da suke cewa magaji mafiyi. Ita kanta Baba Fhatsima tana mamakin yanda Hadiza ta xama kwafinta a kishi. Komansu iri ɗaya ne ta ɓangaren kishi babu inda ta barota saima finta da tayi. Ita kanta da ba dan ta kai zuchiyarta nesa ba, da kuma tunanin goben yaranta ba, da a lokacin da malam zai ƙaro Aure da tuni ta bar auren kwata_kwata. Har gobe zuchiyata tana azabtuwa ainun da zaman kishin da Malam ya haɗata yi da sauran matanshi. Duk da tasan cewar ita da Tasi'u sune fitulun dake haska gidan malam, hakan bai hanata kishi ba. Iya rigima Malam yake kiranta a duk sanda ta murɗa kambun kishinta ta juya mishi baya. Ajjiyar zuchiya ta sauke a daidai shigarta ɓarayin da turakar Malam take. A zuchiyarta take roƙama Hadiza Allah ya bata haƙuri da juriya. Ɗayar zuchiyar tata tana cike da tausayin Hadiza a bisa dakon nauyin kishi da zata ɗauka na iya tsawon rayuwar duniyarta. Da sallama ta shiga falon na malam, yana zaune a kujera mai cin mutum uku Amaryar Malam tana gefenshi tana kiciniyar cire mishi babbar rigarshi. Baba Fhatsima ta haɗiye wani yawu mai kauri, tare da yin wuf ta yi ƙasa da idandunanta. Kunya da nauyin Fhatsima suka kama malam. Cikin dibibicewar data mugun ƙular da Amaryar Malam yace. "Uwar gida sarautar mata, farar mace alkyabbar mata, zo ki zauna Fatsima" Ɗan siririn ɓoyayyen tsakin da a iya kunnen Baba Fhatsima ya sauka Amaryar Malam tayi. Kujerar gabaki ɗaya ta sauka ta barma malam da Baba Fhatsima, ta koma kujera mai cin mutum guda ta kumbura tai suntum. Murmushin takaici Baba Fhatsima tayi, a zuchiyarta tace. "In banda maza da faɗuwar girma ni Fatsima da yaushe zan haɗa gado da yarinya ƴar cikina? Amman su maza basa ko jin kunya, da nauyin manyan yaransu. Wacce iriyar taɓarace Malam bai yi ba lokacin da ludayin Amaryarshi ke kan dawo? Murmushi ta kuma yi mai cike da fassarori da dama. "amarya ina ganin sai kin tashi kin kirawo mun Asshi, da Suwaiba Lokaci yana ƙurewa ya kamata ace sun hallara" Ba dan ranta yaso ba ta fita ta bar Malam daga shi sai Baba Fhatsima ba. Tana fita Malam ya dubeta yace. "Fatsima bakya tsufa ke dai. Wazai ga Tasi'u yace ke kika haifeshi?" "Hmm Malam Baka rabo da daɗin baki, koma kince borin kunya" Da Malam da ita da tai maganar suka kwashe da Dariya. Shi yana dariyar yanda akayi ta ɗagoshi. Ita tana mai dariyar kaji kunya. A haka matan Malam suka shigo suka iskesu. "Au aini naga kamar Amaryar Malam itace da girki ko? In ba ɓatan lissafi nayi ba. Ta faɗa tana kallon Amaryar Malam data cika tana shirin fashewa. Suwaiba ta taɓe bakinta tace. "Girkinta ne, kin mance ita ta wuni tana hidimar yara?" Malam ne ya dakatar dasu ta hanyar cewa. "Yanzu zaku zauna kuji dalilin kiranne ko kuwa zaku tsaya bin ƙididdigar waye me kwana waye marar kwana ne. Wai shin me yasa ke Asshi baki da aikin daya shige na ta da tarzoma ko da yaushe?" Zama ko wacce tayi a kujera. Amaryar Malam ta je ta zauna a kusa daf da Malam. Bai dai ce da'ita uffan ba. Takaddu dunkulallu ya ciro daga aljihun rigarshi ya zube a ƙasa. "Ko wacce ta ɗauki ɗaya ta riƙe a hannunta kafin in gama bayani sai ku buɗe. Sai da kowacce cikinsu ta ɗauka sannan Baba Fhatsima ta ɗauka a ƙarshe. Malam yace. "To wannan ƙuri'ace nayi muku kamar dai yadda nake yi a ko wacce tafiya in ta taso mun. Kuma tunda nake yin wannan ƙuri'ar duk wacce ta ɗauki tafiya bana sakewa da'ita nake tafiya. To a wannan karonma wata tafiyace ta taso babba a gabana ta banbanta da duk tafiye_tafiyen dana saba yi a baya. Naba ko wacce dama ta buɗe takaddarta duk wacce ta ɗauki tafiya to Allah ya ciyar da'ita. Sannan ku sani babu zalunci ko son kai a cikin wannan lamarin Allah shine shaidata. Bismillah ko wacce ta buɗe. Nan da nan ko wacce ta shiga kiciniyar buɗe takaddarta tare da zabarin ganin ta ɗauki tafiya Domin tafiya da malam ana samu alkhairi sosai, kuma macce tana samun lokacin kanta dana mijin nata, soyayya ake darza tsantsa. Cikin sa'a Baba Fhatsima ta samu tafiya. Har cikin ƙasan ranta tayi farin ciki sosai, dan ta jima sosai rabon da ta samu damar tafiya tare da Malam. Kuma a halin yanzu tana cikin yarda dashi. Baba Asshi tafiyar da yayi na ƙarshe wacce ba'ayi wata ba sai yanzu, tare da'ita akaje. Amaryar Malam kuwa sai da ta samu takaddar tafiya sau huɗu a jere ras, Suwaiba ta samu sau biyu a tare. Wannan karon kuma Allah ya ciyar da Baba Fhatsima. "Malam nice na samu tafiya" Bai san sanda murmushi ya subce mishi, farin ciki ya bayyana s fuskarshi ba. Malam har tsaiwar dare yayi kan Allah ya dafa mishi Baba Fhatsima ta samu wannan takadda ta aminci. Kawar da kai Baba Asshi tayi gefe, tare da taɓe bakinta. Malam kuwa yace. "Masha Allah dama kina da paspo ta kwana gidan sauƙi sabida haka ki soma shirin keta hazo" murmushi Baba Fhatsima tayi mai cike da danƙararriyar soyayyar Malam da take ta farfaɗowa. "Allah ya nuna mana lokacin malam. In ka bani dama sai in koma ɓarayina" Kai ya gyaɗa. "Ki isa cikin aminci Fatsima uwar gida ran gida" Ai fitar Baba Fhatsima sai tarzoma ta tashi, daga ƙarshe dai fatattakarsu Malam yayi. Amaryar Malam dake da kwana itama ta bisu tana kuka wai ta yafe kwanan ma baki ɗaya. A wannan daren zukata da yawa a cikin tunani suka kwana, ko wanne da abunda yake tubkewa da warwarewa haka garin ya waye kamar yadda aka saba. Gwadabe:. Tun asuba yake kiran wayar Shafa amman wayar har zuwa lokacin a rufe take. Gashi yana son zuwa ganin Hadiza yaga ya ta kwana. Duk da Auwala ya kwantar mishi da hankali a daren jiya. Tashi yayi jiki a saɓule ya nufi cikin gidan. Yau matan Malam babu wanda ya amsa gaisuwar su Auwala ma balle kuma Gwadabe wanda yazo dandalar arziki. Sai Baba Fhatsima ce dake zaune a dokin ƙofa tana siyan lalle da gishirin lalle akan wata yarinya tace. "Gwadabe yau makara kayi ne sai yanzu ka samu shigowa?" Da biyayya ya zube ya gaisheta, ta amsa cike da fara'a. "Ka shiga Hadiza na ciki, da zazzaɓi ta kwana, likita ma Matar wanku zata kaita" Kai ya kuma saukewa harda sosa kanshi. "Subhanallaah Allah ya bata lafiya, bari in dubata" Ya faɗa da kunya. Shiga yayi ya samu Hadiza a zaune tana shan kunu. Ƙurama juna idanu su kayi na daƙiƙu. Ita ta rigashi sauke ido. "Ina kwana Yaya Gwadabe?" Bai samu damar amsawa ba, waje ya samu ya zauna a ƙasa ƙur idanshi a kanta. "Ina roƙon Allah yasa ba maganata ta jiya bace sanadiyyar ciwonnan naki ba Hadiza?" Bai jira ta amsa shi ba dan bai tambayeta yana nufin saita amsaba ya ɗaura da faɗin. "Wallahi ba dan Baba magaji ya tozartaki ko ya ƙasƙantar da darajarki bane yasa yai miki zaɓin Gwadabe ba. Nima ba dan tayin da yaimun bane yasa na amsheki ba face kin yi mun kuma naji zan iya rayuwar aure dake. Yanayinki da zubinki yana mun kama da na matata Iyabo sosai. Ki fahimceni auren zumunci cike yake da tarin hikimomi. Itama fa bawai ina nufin bana sonta bane A'a itama inai mata kalar nata son daban. Hatta tsohuwar matata gurbinta shine a ƙasan zuchiyata. Ki kwantar da hankalinki kinji?" Tunda ya soma magana zuchiyarta ke lugude. Musamman da taji matsayin da Iyabo ta wawashe a rayuwar Gwadabe. Sai Allah ya sadamu ranar Monday da izinin Allah danjin yadda zata kaya. Ki faɗi abinda kika ɗauka na darasi a wannan labarin duk da bamu yi nisa ba. [8/9, 6:47 PM] +234 803 969 6400: https://chat.whatsapp.com/Dqaioj0tydVHQGo5zoG0lm NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE BOOK 2 5 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* _Assalamu Alaikum barkanmu da juma'a. Iyabo tana godiya a bisa karɓar labarinta da kukayi hannu bibbiyu_ Lokaci ɗaya taji kishin Iyabo ya soki murfin zuchiyarta fiye da kishin wacce za a haɗasu zaman kishin na gasken_gasken. Bata sami zarafin furta mishi kalma ba Auwala da Anty Badi'a suka shigo a tare. "Hadiza in kin shirya muje Yayanku ya rage mana hanya ko?." " to" Ta furta tana kallon Gwadabe, wani irin kallo daya kasa fahimtar fassararshi. A kunyace ya gaishe da Anty Badi'a, ta amsa cike da kulawa. "Gwadabe maza muje Mammada na jiranmu kasan fa yau muna da aiki." Cewar Auwala kenan. Kafin ma ya miƙe Malam Magaji ya iso dokin kofar yana faɗin. "Yarannan har yanzu basu wuce aikin ba, Auwala me kuke yi a ƙunshe a ƙurya haka?" Da sauri suka fito, sumi_sumi sukai ma iyayen sallama suka fice a gidan. Cikin sa'a Gwadabe ya gwada sake kiran layin Shafa ya samu a buɗe. Sai dai harta gama kuka ta tsinke ba a ɗaga ba. Yana sauke wayar a kunnenshi sai ga kiran Tamu ya shigo. "Abokina yau kaine da kira sassafe haka, ya kwanan iyalin kuma?' Cewar Gwadabe daya tari numfashin abokin nashi ta hanyar rigashi magana. Ajjiyar zuchiya ya sauke yace. "Tun jiya Ayashe ta sanar dani Shafa nata faman kuka ta kulle kanta a ɗaki. Ko da aka wayi safiyar yau taƙi cin abinci, taƙi zuwa wajen aiki. Shine nasa ita Ayashe tai kiranta dan inji menene. To ta dai ƙi yin magana ma, bansan ko kana da masaniya akan kukan ba, kasan yarannan fa da zafafawa akan soyayya, dan naga ta ɗauki lamarinka da girma. Kasan mata da surutu ina jin labaranka sosai ta bakin Ayashe" Jim Gwadabe yayi kawai yana mamakin halin da Shafa da Hadiza suka shiga a kanshi, ya ɗan shafo ɗan siririn hancinshi tare da shiga zancan zuchi. "Ohh ni Gwadabe ni ba kyau mai suna kyau ba, ni ba tsayi ba, ga tumbi, ga ƙaton kai. Amman akaina waɗannan matan suke shiga damuwa haka? Dama_dama Iyabo na cancanci ta soni, duba da yanda tasha naci a wajena, da irin yanda na jajirce kan soyayyarta. Amman waɗannan haɗani dasu dukka akayi, bawai ni nace ina sonsu ba." "Kana jina kayi banza dani Gwadabe ko network ne, ko ko dai wani rashin kunya Shafa tayi maka?" Tamu ya tsinke mishi zaren zantuttukam zuchin shi. Da sauri yace. "Kai kasan komai Tamu akan Hadiza da Baba Magaji ya bani bayan na baro najeriyane. To ita Hadiza bata san da zaman Shafa ba, kamar yadda Shafa bata san da zaman Hadiza ba." Nan dai ya kwashe labarin duk yadda ta kasance musu a jiyan. Tsaki Tamu yayi kawai tare da cewar. "Shirmen banza harma ka tunzurani ƙila saina zaneta ma. Yanzu akan wannan maganar ne duk ta takure kanta?" "Kul wallahi kar ka soma dukan mun mata ni dai na faɗa maka dan ubanka" Dariya suka yi Tamu yace. "Wannan siriki kwai fitsararren maras kunya" Dariya suka sake sawa, kafin Tamu yace. "Yaushe zaka shigo mana najeriyar ne Gwadabe, ka gujemu. Ko dai har yanzu damuwar rashin Iyabo ne ya hanaka zuwa? Mu kuma cike muke da kewarka, ko babu komai ya kamata kazo kaga yara" Gwadabe yaji wata kewa ta kamashi, take yaji yana sha'awa da son ganin abokan nashi da ma yaranshi. "Tamu zan zo zuwa ƙarshen wannan watan da muke ciki, kaga yau wata yayi goma biyar, yana kaiwa ƙarshe zan zo in duba ku. Ya yaran?" "Yara kowa lafiya lau sunata karatunsu hankali kwance. Toye ma dana shiga ƙauye naga yayi noman masara shi da yaron Bara'u baka ga yanda masarar tai kyau ba. Na lura yaron yana da mai da kai akan abinda yake gabanshi, shi kanshi Bara'u ya yaba" Sun jima suna hirarsu ta abokai kafin daga bisani su kai sallama. Ko da yaje wajen aiki daya fito cikin ramin haƙar zinariyar dan hutu sai ya kira lambar Shafa, bata shiga ma baki ɗaya. Da ƙyar ya samu dai ta shiga, kuma yaci sa'a aka ɗauka. Daga nan zancan fishi ya ƙare, bayan ƴan bayanai daya yi mata, da kuma kalamin kwantar da rai, sai suka balle da hirar soyayya, wanda rabi da kwatan hirar Shafa ke yinta, shi dai yana dai ƙarfafa mata guiwa ne. Bayan sun yi sallama ya kira Hadiza ma yaji yaya jikin nata tare da ɗan taɓa hirar da rabinta da kwatanta labarin zafin da taji a zuchiyarta ne, shi dai aka barshi da aikin rarrashi. Jigum ya zauna yayi tagumi bayan gama wayarshi da Hadiza. Kanshi ya ɗauki caji ainun. Harga Allah shi dai bazai iya gane yana son su Hadiza ne, ko kuma yana kallon darajar waɗanda sukai mishi tayinsu ne ba. Domin mace ɗaya tilo Iyabo itace a zuchiyarshi abadan. Yasan abune mai wuya dawowar Iyabo cikin rayuwarshi. Yana fatan inya shiga Najeriya Allah ya haɗa fuskokinsu ko da a hanya ne. Yana kuma da burin son ƴaƴanshi su yi rayuwa a gefenshi damin ya ɗauke musu raɗaɗin maraicin uwa a rayuwarsu. Mammada ne ya dafa kafaɗarshi, yana zaune a gefenshi shi bai ko ji tawowar tashi bama. Abinci ya miƙa mishi, garau_garau irinta leburori irinsu, yasa hannu ya amsa. "Menene Gwadabe, kaddai batun Hadiza ne duk yabi ya dameka?" "A'a wallahi Mammada tunanin rayuwa kawai nake yi da rashin daɗin aikinnan, tare da tunanin yarana da basa kusa dani anan" Ɗan murmusawa yayi, sai da ya ciko garsu_garau a cokali ya danna a bakinshi dam kafin yace. "Wannan ai mai sauƙine Gwadabe, kai da kake jarumi me auren mata biyu, ai zasu riƙe maka yaranka wannan bama wata matsala bace" Abincinshi yaci gaba da dannawa a baki bashi da damuwar komai. Sai Gwadabe yaji dama ace shine Mammada da yaji daɗi. Wunin wannan rana da tunanin Iyabo da yaransu Gwadabe ya wuni. Yayi ƙoƙarin samun layin Bara'u ma dan ya sanar mishi da batun zuwanshi, amman dai basu sami damar jin juna ba. Kamar dai yadda aka saba bayan isha Gwadabe ya aiki yara su kai mishi kiran Hadiza. Yana zaune a saman dakali tazo ta sameshi, bayan sun gaisa yayi mata ya jiki, sai shiru ya biyo baya. Dukkansu a cikin tarawa da ɗabewa suke. Sai dai tunaninsu ya sha banban dana juna. "Menene ya dameka wanda harya kasa ɓoyuwa akan fuskar taka, ko baka samu damar jin muryar Shafa bane?" Ɗagowa yayi suka haɗa idanu. Ɗan gajeren murmushi yayi mata tare da cewa. "Babu mamaki dan naji sunan Shafa raɗau a bakin ki, tunda Malam yasan sunan. Yaya jikin naki da sauƙi, kuma kinsha magungunan da suka baki? Ya jero mata tambayoyin da yake tunanin zasu jaye hankalinta daga barin batun Shafa. Amman sai ta jefo mishi wata tambayar da cewa. "Ni ko zan so ganin tsohuwar matarka ko da a hotone domin inga da abinda tafi sauran mata" Ta ƙarashe maganar da taɓe bakinta. Anan ne taga ya gintse fuskarshi dukkan annurunshi ya dakata. "Kar ki kuma kawo maganar Iyabo anan wajen. Ki tsaya dai iyakar matsayinki da kike dashi a zuchiyata. Batun ita kanta Shafa ki shafe shi a kan ki, ni dake mu tattauna akan iyakar abinda yake gabanmu. Kuma ko ita Shafa in tayi mun magana a kan ki, ko Iyabo, dakatar mata zanyi domin babu abinda zaku ji daga gareni. Dukkanninku kuna da matsayi na musamman a zuchiyata" Ajjiyar zuchiya ta sauke. Ranta yayi matuƙar ɓaci ainun, idanunta kuma sun rufe da kishi. Amman a zuchiyarta tasan ita ke da laifi da bata cakalo zancan ba da ba'ayi ba ma balle har ya tsayar mata. "Karshen watannan inaso zan leƙa Najeriya in dubo su Babala da yaran wajena in Allah ya nuna mana da rai da Lafiya." Cikin dakiya tace. "Allah ya nuna mana lokacin" Ya amsa mata da "Ameen" Shiru ya sake wanzuwa a tsakaninsu na kusan minti biyar cur, Gwadabe ne ya daure yace. "Kishi yau ya hanaki yin magana ko Hadiza? Bansan me yasa kike damun zuchiyarki har haka ba wallahi. Mata ku dinga sassautama rayukanku akan kishi ko a zauna lafiya " Kallonshi tayi ido a cikin ido tace. "Ashe kishin abinda kake so yana iya zama illa ni ban sani ba? Ai na ɗauka wanda yake da girman daraja ake kishi ba wanda bai isa ba" Kai ya dafe tare da lumshe idanunshi. "Yi haƙuri Hadiza kinji. Bance laifi bane dan kin nuna kishinki a gareni ba. Amman tunda lamarinnan ya faru baki bar zuchiyata ta zauna lafiya ba. Kinga na dawo a mugun gajiye yau. Hira dake yana warware dukkan gajiyar dana kwaso. Amman yau ke da kan ki kike shirin labto mun wata gajiyar ta daban ma" Yayi maganar da irin sigar daɗin bakin maza mai zurma matan da basu gane kan rijalu ba ( Ummu nabeeha ana magana) Jin ya faɗi haka ne yasa ta ɗan sassauto har suka taɓa hirar dai ba wani armashi. Haka kwanaki sukaita tafiya dare ya shigo, haske ya maye gurbinshi. Gwadabe sai ɗan siyan tsaraba yake yi yana adanawa kafin zuwan lokacin tafiyarshi. Baba Fhatsima itama sai shirin tafiya take ta tayi. Matan gidan kuwa sai tashin hankali ya ƙaru a garesu. Cikin kwana goma suka shirya tsab da yamma Tasi'u ya ɗaukesu izuwa Airport. Al'amarin daya mugun tada tarzoma mai girma a gidan bayan tafiyarsu Malam. Dan Baba Asshi tana kuka a tsakar gida ta dinga kiran iyayen Baba Fhatsima tana kunduma musu ashariya. Hakanne ya tunzura Hadiza da su Auwala da shigowarsu kenan. Al'amarin dai baiyi daɗi ba sam, Yaya Tasi'u ne ya dakatar da faɗan ta hanyar yin hargagi ga ƙannen nashi akan kowa ya kama gabanshi. Dan samarin ɗakin Baba Asshi ma sun shiga rikicin. "Ku yi haƙuri Baba. A dai dinga kai zuchiya nesa. Ya kamata ace yanzu maƙota sun dena jiyo sautin faɗa da ashariya daga gidan Malam. Wannan al'amarin tun muna yara aketa faman yinshi har yanzu tsugunne bata ƙareba. Ya kamata ace mun haɗe kawunanmu tun kafin wankin hula ya kaimu ga dare" Cewar Yaya Tasi'u kenan cikin takaici da baƙin cikin irin rarrabuwar kawunan dake cikin gidansu. Inama zasu yadda a haɗe a zama abu guda. Amman kash an bar kari tun ran tubani. Malam shi ke da sa sannu a faruwar komai, kuma yafi kowa da kowa son ganin ya haɗe kan ahalinshi sun dawo abun sha'awa a yanzu da yake ganin kamar wankin hula na shirin kaishi dare fa" BABA FHATSIMA A hotel ɗin dake bayan harami aka sauke Malaman da aka zaɓe aka biya ma aikin umara su da iyalinsu. A baya malam ya samu ire_iren kyautuka irin wannan, kujerar aikin Hajj ma da suka yi da Baba Fhatsima na farko wani ɗan siyasa ne Babba ya bashi, a sakamakon adda'a da malam yake taimaka mishi dashi, kuma yana ganin buɗin haka. Sun je umara da dama, gashi a wannan karon ma Allah ya nufa da'itan za'a sake komawa. Zaune take akan kujerar dake ɗakin hotel ɗin. Tana jiyo zubar ruwan wankan malam a ƙasa. Zuchiyarta sai take jinta fes Kamar babu wata damuwa dake ƙunshe a cikinta tsawon shekaru. Tunani ta faɗa mai zurfi. Tana tuno lokacin da suka sauka a wannan hotel da suke ciki a shekarun baya. A lokacin Malam yana ji da'ita yana girmamata fiye da tunanin me tunani. Bata mance wasu kalamai da malam ya faɗa mata a ranar da suka shigo makkah da daddare bayan sun gabatar da mu'amalar aure ba. "Fhatsima samunki nasarane babba a cikin rayuwata. Wallahi Fatsima jina nake yi tamkar wawa soko muddin bana tare dake. A duk lokacin dana kalli ƙwayar idanunki su kaɗai ka iya sauke mun dukkannin damuwata, duk girman matsalar da nake ciki. Ƴan siyasar da muke mu'amala dasu da dama sun sha bani ɗiyoyinsu in aura. Amman Fhatsima nasan ni naki ne ke kaɗai bazan iya haɗa soyayyarki da ko wacce mace ba a faɗin duniyarnan da muke ciki ba." Fitowar Malam ita ta katse mata zaren tunaninta ta dawo duniyar mutane. Ido malam ya zuba mata ƙur, jin kaifin idanunshi yasa ta ɗago kai suka haɗa idanu. Amman me sai malam yaga kwantaccen hawaye a guraben idanun Fhatsima. Zama yayi a kusa da'ita ya kama hannunta dukka biyu, ɗumin tafukan hannun juna ya ratsasu sosai. Ƙunshinta yake bi da kallo yanda aka jera salateb ( suffa,) akayi ado dashi cikin hikima, lallen ya sake fito da kyawu da hasken hannun nata. "Fhatsima wannan lallen nawa ne akayi mun?" Ya faɗa a mugun raunace dan ji yake kamar yayi kuka. Shi kaɗai yasan irin gasuwar da ruhinshi da gangar jikinshi take yi. Itama a sanyaye tace. "In ba kai ba Magaji wa zanyi ma lalle uban ƴaƴana?" A sanyaye cike da kunya yace da mamaki ya dubeta dan yasan in tana cikin yarda dashine har take iya kiranshi da Magaji a keɓe, amman dama a cikin mutane da cikin fishi Malam duk take kiranshi." "Fhatsima yau ni kika kira da uban ƴaƴanki, kuma kikace domina kikai wannan lallen?" Murmushi tayi tace. "Magaji ai har yau har gobe ruwa na maganin dauɗa" Farin cikine marar misaltuwa ya lulluɓeshi. "Fhatsima nayi kewar kasancewa tare dake, nayi kewar rashin samun cikakken lokaci kamar yadda kika sabarmun, nayi kewar kulawarki, nayi kewar tausasamun da kike yi Fhatsima. Na sani ni nayi kuskuren ruguza amincin dake tsakanina dake. Wanda in kin tambayeni dalili bani dashi wallahi. Nayi nadamar komai, ina takaicin faruwar komai Fhatsima. Hawayene tab a guraben idanunshi, yana ta girgiza kai irin na kaico. "Magaji cutuwa iya cutuwa nayi, tun daga lokacin da abubbuwa sukaita faffaruwa dauriyaa kawai nake yi, da ba a iya hawan jini abun zai tsaya ba, numfashina zai rabani dashi, in Barka a duniya da matan naka na so" Ɗan murmusawa yayi kawai. Baice komaiba ta ɗaura da cewar. "Na fuskanci wulaƙanci da matsi wanda ni kaina bansan ina da irin wannan haƙurin ba. Soyayyarka data yaranmu ce kaɗai tasa naci gaba da rayuwa da matanka. Burina shine ace da kaina naba ɗiyoyinmu tarbiyya a bisa doron alƙawarin da nayi maka tun kafin aurenmu. To Alhamdulillah na sauke nauyi" "Gashi ƴaƴan da suka fito a ɗakinki sun kasance sanyi da hasken idaniyata Fhatsima. Sun kasance abun alfahari kuma jagorori. Wannan kaɗai wata babbar nasarace a gareki, kuma hakan ya ƙara tabbatar dake a matsayin shugaba kuma uwar gida a gidan Magaji. Ko wacce mace da ƴaƴanta, dani kaina Magaji a cikin rigar alfarmarki nake Fhatsima " Idanu ta ƙura mishi tana mishi dariya shima dariyar yake yi. "Magaji kai da kaya mallakar wuya ne. Kuma ba'a hana ma ba da rago fata, tuwo baya canja sunanshi. Yarannan baka ragesu da komai ba tun yarintarsu har zuwa yanzu da nake wannan maganar. Fatana Allah ya haɗe kan iyalin naka baki ɗaya. Duk da kai da kan ka ka farraƙa haular gidanka, kasan....." "Ya isa Fhatsima kar ki rusamun farin cikin dake ƙunshe a raina" Ya katseta da hanzari. "Inaso ki tsaya mun kuma ki taimaka mun ke da Tasi'u da Jamila mu haɗu mu haɗa kan iyalinmu. Abinda ya wuce ya wuce, kece zaki taimaka komai ya gudana. Sannan haɗe yaran da matansu ni inata jaddadawa kamar zai iya gyara lamarin. In kan yaran ya haɗe, dole iyayen su shafa ma kansu ruwa. Asshi ce dai nasan zata ba da wahala. Ammam fa a shirye nake tsab da in rabu da duk matar da zata kawo mun taurin kai. So nake in gyara abinda na ɓata tun da rayuwata kar in bar baya da ƙura." Ajjiyar zuchiya Baba Fhatsima ta sauke. Yayin da take hasko abubbuwan da suka zama sune sababin faruwar waɗannan matsaltsalu na gidan Malam. Gani take yi kamar yanzu suke faruwa. "Baki ce uffan ba Fhatsima" Ya jefeta da tambayar. "Malam a ɗayan biyu ne wannan haɗe yaran da kai da Tasi'u kuke ganin zai yi tasiri wajen kawo soyayya da shaƙuwa a tsakankanin yaranka. Hakan zai iya faruwa, ko kuma hakan ya sake farraƙa kan yaran, ko da ta Hanyar matayensu, ko ƴaƴan da zasu hayayyafa. Malam wannan lamarin babbane. Amman mu dage da roƙon rabbil izzatu. Gamu a ƙasa mai tsarki mu dage da adda'a Allah yasa hakan ya zama matattakalar da zamu hau tsanin da zai wanzar da farin ciki a tsakanin Ahalinka. Sannan sai ka sanya dokoki masu tsanani, kayi ƙoƙarin dogewa akan dokokin. Kar ka faɗesu ba tare da ka basu mahimmanci ba, wannan raunin naka yana ɗaya daga cikin abinda ya soma kawo rarrabuwar kai a tsakankanin Ahalinka." A taƙaice dai sun jima sunata tattauna yanda za'a ɓullo ma lamarin. Sun yi adda'a sosai. Malam da Baba Fhatsima sun sasanta kansu sai ɓarzar Amarci ma suke yi abinsu. Sai yanzu ne Malam ya dawo cikin nutsuwa da hayyacinshi. Ya saki ajjihu wajen ganin ya kyautatama Baba Fhatsima, duk da ragowar mata da ƴaƴanshi ma bai barsu a baya ba. Gwadabe. Ana gobe Gwadabe zai kama hanyar Najeriya. Sun sha hira ainun da Hadiza da ƙyar ta barshi ya samu ya shiga ciki yaci gaba da shirya kayan tafiya. Kishine ɗamfare a ƙirjin Hadiza dan ita gabaki ɗaya a tunaninta Gwadabe baibai kawai ya ninketa amman wajen Shafa yake son zuwa. Shadda dalleliya da ƴan kunne Hadiza ta bayar a kaima Babala, ta bada agogo mai kyau tace ya kaima Shafa. Anty Badi'a kuma ta ba da takalmi da mayafi tace akaima Babala. Yaya Tasi'u kuma kuɗi ya bayar akai mata, sai ƙarin guziri da yaba Gwadabe. Sassafe kuwa Mammada ya rakashi tashar mota. Motarsu ta ɗaga zuwa Najeriya. A garin Kano ta dabo tumbin giwa Gwadabe ya sauka. Misalin ƙarfe tara na dare dake motarsu ta samu matsala a hanya sun daɗe a yashe a titi sosai. Sakkowarshi daga mota ita ta kara mishi damuwar rasa Iyabo da yayi a rayuwarshi. Gashi dare yayi, kuma bazai taɓa iya taka kafarshi zuwa gidan Yaya Hambali ba. Bashi da zaɓin daya wuce ya nemi gidan kwana a tasha, gobe sassafe yana son ya leƙa gidansu Iyabo ko Allah zai yi ko juna su gani, su gaisa kafin ya tafi. "Malam muna da ɗakin saukar baƙi in kana da buƙata. In kuma a Kano tafiyarka ta ƙare akwai tasi da Bus a bakin tasha zata kai ka duk inda kake buƙata. Cewar wani ɗan yuniyon. "Inada buƙatar ɗakin, Takai zan wuce zuwa gobe da safe dan Allah" "Nera hamsin kuɗin kwana, in bawali zaka yi a banɗaki kuma nera biyar, ba haya nera goma, wanka nera ashirin, ruwan zafi ma ashirin." Wani ɗan yuniyon dinne yace. "Haruna ka fiye surutu, ka ɗauki jakarshi dallah ka rakashi masauki" Wanda aka kira Haruna ya tuntsure da dariya yace. "Ai gara muyi gwari_gwari dai." Jakar kayan Gwadabe ya saɓa a bayanshi yace. "Biyoni muje in kai ka" A baya Gwadabe ya bishi zuwa can cikin tashar, wani gida mai kama dana masu zaman banza suka shiga. Maza da mata, da ƴan daudu ne a cakuɗe suna caca, masu ƙidan garaya kuma sai kiɗa suke yi, ga masu shan tabar sigari, ga masu cin goro da tomtom kowa dai da abinda yakeyi. Ƙyauran wani ɗaki Haruna ya buɗe suka shiga. Matasane a ciki fin su takwas, wasu sunyi bacci, wasu na bacci, wasu abinci suke ci. Tabarmace malala a ɗakin, sai kayi matashin kai da buhun kayanka. Gwadabe bai gama ƙarema dakin kallo ba Haruna ya miƙo mishi hannunshi. Nera hamsin ya bashi. "To ka raɓa ta can lungun ka kwanta. Kana buƙatar abinci ne?' "E ina buƙata, amman tuwo nake so" Haruna yace. "Tuwo miyar kukace kaɗai tayi ragowa. Ko wacce malmala nera ashirin ce, nama kuma ko wanne tsoka nera goma, man shanu ko wanne cokali nera biyar" Dariya Gwadabe yayi, duk da damuwar da yake ciki. Shima harunan dariya yayi. Nera ɗari ya miƙa mishi. "To a haɗa komai da komai na ɗari harda ruwan sha" Zaman Gwadabe ke da wuya sai ga kiran wayar Shafa. "Assalamu alaikum Shafa barka da dare, har izuwa irin wannan lokacin baki yi bacci ba?" Ɗan murmusawa tayi, cikin taushi da zaƙin murya tace. "Na kasa baccin inata jiran kiranka kace mun ka isa Takai in samu nutsuwar ruhi tukunna. Jin shiru ne yasa nace dai bari in nemeka" Ɗan murmushin wahala yayi mata yace. "Ayya. Kin ganni a Kano bamu daɗe da shigowa ba ma. Sai zuwa gobe in Allah ya kaimu zan karasa takai ɗin." Iska ta fesar daga bakinta. "To Allah ya nuna mana. Bari in barka ka samu ka huta, zuwa safiya in ka isa Takai mayi waya" Bai bata amsaba ƙit wayar ta ɗauke chaji ya ƙare, a ajjihu ya wurga wayar ya samu ya gyara zaman ƙatuwar jakar buhunshi. Wata budurwace ta shigo mishi da tuwo. Bayan ya gama ci kuma sai yayi jigum a zaune yanata faman tunanin yadda za'ayi gobe kafin tafiyarshi yaga Iyabo ko da basu yi magana ba. Wata zuchiyar tace dashi."ƙila ma tana can gidan mijinta ta mance dakai" take gabanshi ya tattake ya faɗi. Da wannan zulumin ya kwana. Sassafe bayan sallar asuba ya fice a tashar bayan yaba Haruna ajjiyar jakar kayanshi. Kai tsaye motar layin su Iyabo ya shiga. Tun daga hango gidan damuwarshi ta sake yin tsanani, bugun zuchiyarshi yaci gaba da ƙarfi. Iyaa Debisi ya hango tana ma yara masu kawo niƙa niƙan wani abu haka kamar gero, kamar dawa. Yana isa wajen ta kalleshi ta zuba mishi harara harda tsaƙi, ta mayar da hankali a kan niƙanta. Shi ko ƙiƙam yayi yana jiran ta kashe injin ɗin su gaisa. Amman bayan fa gaisuwar baisan me zai soma cewa ba. Ya [8/12, 5:09 PM] +234 803 635 0240: NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BOOK 2 6 Yaya Hambali ya gano a zaune ya jingina da garu, Babala tana zaune a kujera, Auta na ƙasa a gefen ƙafar Babala. Ɗakin Babala yasha gyara kujerunma sababbi fil, hatta labule sababbi ne aka zuba. "Babala lafiya na ganku kunyi jigum? "Hmm lafiya ba lafiya ba Gwadabe. Kaine a tafe sassafe haka?" Babala ta bashi amsa. Waje ya samu ya zauna, Babala ya soma gaisarwa, kafin Yaya Hambali. Babu yabo babu fallasa ya amsa, dan ko juyowa ya kalleshi bai samu wannan darajar ba. Auta ce tace. "Yaya Gwadabe sannu da zuwa" Jiki a mace yace. "Yauwa Auta, ya mai gidan naki?" Shiru bata amsaba, Babala tace. "Yaya ka baro su Yaya Magaji, da fitinannun matanshi marasa daraja?" Ɗan murmushi yayi, a ranshi yace. "Babala ba zata canja ba" A fili kuma yace. "Malam yana Saudiyya shi da Baba Fhatsima yau kwanansu biyar ma. Duk kowa yana lafiya, sunce ma in gaisheki" Mikewa tsulum Yaya Hambali yayi. "Babala ki gama dashi na dawo in kum gama. Dan bazan iya zama inuwa ɗaya da wannan kangararren yaron marar jin maganarki ba" Yana gama faɗin haka ya fice, Gwadabe ya bishi da idanu galala. Babala ta amsa mishi da cewa. "Kangararre fa, yaro aita nuna mishi annabi yana runtse idanu. Ni kaga banyi ma tunanin zai sake zuwa dubamu ba" Yaya Hambali dake tsaye yana sa takalmi yace. "Sabida Bara'u ƙanin ubanshi yazo, da wannan ɗan nashi me cakuɗe da jinin yarbawa ai" Yana gama kunna Babala yayi tafiyarshi. Ai fa nan Babala ta inda take shiga ba tanan take fita ba. "Shima Bara'un ashe kangararrene irinka?. Yasa wannan yaro ɗan wajen beyerabiyar tsohuwar matarka a makarantar boko Har gida naje na samu Sakina matarshi nace da'ita ina son ganin shi Bara'un. Wallahi ko da yazo na zayyanama Bara'u bana son wannnan ɗa yayi boko. Yaronnan ya shafa toka a idanunshi yace in yi haƙuri dole a yanzu yara suna buƙatar ilimin boko. Ko da wanku ya shiga zancan ƙarshe ma Bara'u ce mai yayi ai shima yaranshi na zuwa boko dole shima wannan ɗan yarbawa yayi boko. Zan yi maganinku dukka, har wajen uwarshi naje na kai ƙararshi ai" Gwadabe dai yayi jim yana saurarenta sai zuga faɗa take yi. Sai da ta gama tayi mai isarta yace. "Ayi haƙuri dai Babala dan Allah." Hannu yasa a ajjihu ya zaro kuɗin da Yaya Tasi'u ya bashi ya kawo mata." "Ga wannan inji Yaya Tasi'u yace a kawo miki, matarshi ma ta bada tsaraba" Hannu tasa ta fisge kuɗin da ƙarfi. Gwadabe dai in da sabo ya saba. Tsarabar daya tawo dashi duk ya cicciro ya baza a gaban Babala. Yadinga mata bayanin mutanen gida da za a rarrabama. Ya ware nata dana Auta dana Yaya Halima. "Banga na yayyenka su Fodiyo ba, balle nasu Da u. Me kake nufi kenan Gwadabe?" Sauke kai yayi ƙasa yayi jim kaɗan. "Kiyi haƙuri nan gaba in zan tawo zan tawo musu dashi, amman yanzu kam babu nasu" "Baka isaba dan ubanka. Yayanku meye a rayuwarnan bai yi maka ba? Ya ciyar dakai ya shayar dakai, yayi maka sutura, ya goyaka a bayanshi ya kai ka makarantar allo data boko da guminshi. Yau sabida wata ƴar iskar beyerabiya shine kake shirin yanke halaƙarka da ƴan uwanka maza? To ni zan tattare duk abinda ka bani in basu bana buƙatar ka sake kawo mun komai madamar ba zaka baiwa ƴan uwanka ba. Kasan ai sunfi ƙarfinka ta ɓangaren arziki. Yanzu haka duk mota suke ja har Da'u. Jebeka kai a fige a bushe, sai uban naɗin buzaye a ƙaron kanka. In baka yi wasa ba ma a haka zaka ƙare Gwadabe" hawayene suka gangaro da gudu zuwa kan kuncinshi. Ya kasa furta daidai da kalma. "Bama son duk abinda zai fito daga hannunka Gwadabe. Munfi ƙarfinka,tun da majina a hancinka nake juya kuɗi. Da wasa kar kayi gigi ƙafarka ta tako gidana bana son yin hulɗa da kai har gaban abada mitsiyaci" Cewar Yaya Hambali dake tsaye a dokin ƙofa, yaji dukkan tattaunawar Gwadabe da Babala kan tsaraba. Babala ta turo ma Gwadabe tsarabar da yayo mata dana su Yaya Halima. "Gashi dani da ƴaƴana bama buƙatar komai daga gareka. Wannan dai da aka baka saƙo ka kawo mun na karɓa. Matan gida kuma kaje ka rarraba musu da kan ka" "Babala kiy mun rai kiyi haƙuri. Yaya Hambali kaima kayi haƙuri. Duk tsawon watanninnan tsarabarnan nake ta siye ina jefarwa. Iyakar abinda kuɗina ya iya siya kenan." Ya faɗa cikin sigar rarrashi. Kamar sake tunzura Yaya Hambali yayi ma. "Shine nace maka kaine mitsiyaci Gwadabe. Dan wannan duk tsarabar bata wuce in siyeta a take in bayar da'ita sadaka ba" Babala tace. "Faɗa mishi dai. Baka ga yanda arzikinshi yaci uban nada bane. Gidanshi na kano an ruguje ya dawo gidan bene Ai kaga yanda gidannam ya dawo ko gidan mai gari albarka, ga babbar motarshi a ƙofar gida" Gwadabe yana zaune suka ƙare mishi tanadi tsab, ko tari baiyi ba, idanunshi sun kaɗa sun zama jawur. Yanzu iyayenmu sun zama abinda suka zama. Nuna fifiko akan ƴaƴansu masu sukuni akan waɗanda su Allah bai basu ba. Miƙewa yayi da tsarabar matan gidan ya kaima Goggo Yabi yace ta raba a tsakankaninsu. Bayan ya dawo ɗakin Babala ne tace. "Ya batun Aure, ko kanaso kace ba zaka sake aure bane tunda ka rabu da ƙanwar uwarka Iyatu? Ga Laila tayi aurenta, yarinya da kyanta Allah ya taimaketa ta auri mashahurin ɗan siyasa, baka ga gidanta ba." "Aure zanyi Babala. Baba Magaji ya haɗani da ƴarshi Bazawara Hadiza harma mun sasanta kanmu, Lokaci kawai ake jira. Kuma..." Ta katseshi da cewa. "Kuma me? Dama shi Yaya Magaji abinda yake so kenan shi yasa ya goyi bayanka ka bijere akan auren Laila, ashe tashi ƴar yake ma tanadin talaka kamarka? Na lura so yake ya yanke zumunci damu, domin matsawar Iyatu taji wannan batu zata yi fishi. Dan kawai Allah ya jarabceta da ɗiya me ciwon sata." Nan Babala taita jujjuya zancan. Gwadabe na son ya faɗa mata batun ƙanwar Tamu, amman tsoro ya hanashi, dole ya ja bakinshi ya tsuke. "Babala ni zan shiga ciki in yi wanka. Jazuli yana ciki ne?" Ya tambaya da dariya a ƙoƙarinshi na danne damuwar data addabi zuchiyarshi. "Ka dai je ɗakin nasan a buɗe yake. Wake zama baya neman arziki? Jazuli yana Kano Yayanku ya buɗe mishi shago, ya kan dai shigo Takai lokaci zuwa lokaci" Kai kawai ya girgiza ya ɗauki jakarshi yana shirin fita Babala tace. "Kazo ka kwashi tsiyarka fa Gwadabe" Fita yayi tare da cewa. "Ni lada nake nema. Ko zubarwa kikayi daidai ne Babala" Har yabar barayin bai dena juyo sababin Babala ba. Wanka yayi ya shiga ɗakin Jazuli ya zauna a bakin katifa yana mai cike da zulumin irin furucin da Babala ta daɗe tana jifanshi dashi na rashin arziki. Gashi duk abinda yasa a gaba baya samun nasara sam. Ko haƙon zinari ya shiga rijiyar zaiyi. To sai dai fa yasha wahalar banza. Sau huɗu ya taɓa samun dutsen zinare ƙananu suma. Amman Auwala da Mammada sau nawa suka samu, sai dai fa in an siyar su ɗan tsakura mishi na kashewa. Dan aikin haƙan zinare ba aiki bane na wasa, balle har wanda ya haƙa ya baka kuɗi me yawa, aikine mai cinye ƙarfi da ƙuruciya sosai. A hakanma yaga ƙoƙarin su Auwala da suke sammishi wani abun. Dan kullum fa a cikin shan ƙwayar bature suke maganin ciyon gabɓai. Ga auren mata biyu a gabanshi, bai tara ba bai ba wani ajjiya ba. Atampa biyu kawai ya ajjiye. Auwala kuwa ya gama haɗa kayan akwatinshi tsab, takalmane kawai ya rage. Iska ya furzar a bakinshi a fili yace. "Anya bazan fito in faɗa ma Tamu gaskiya ba kuwa? Ni bani da ƙarfi, kar in auri mata biyu in zo in gaza wajen kulawa dasu. Yana da kyau Tamu yasan yanayin samuna fa. Amman bari inje in samu Bara'u inji ta bakinshi" Zuruf ya miƙe cikinshi ya wani juya mishi. Sai lokacin ya tuna ashe fa baici abinci ba ma. A ƙofar gida ya tarad da Yaya Hambali da abokinshi Inusa yaron mai gari. "Gwadabe kaine a garin namu?" Ya tambeshi da fara'a. Fuska Gwadabe ya sake ya miƙa ma Inusa hannu suka gaisa. "Ciwo kayi ne Gwadabe, kai kaga yanda duk ka faɗa kuwa?" Kai Gwadabe ya sosa kana yace. "Sha'anin rayuwa ce kawai Yaya Inusa. Yau da gobe bata bar komai ba, a dai samu a adda'a" Girgiza kai yayi cikin tausayawa yace. "Allah ya rufa asiri. Zamu yi magana da Hambali muga me ya dace a taimaka maka dashi" Buɗar bakin Yaya Hambali yace. "Da za a taimaka mishi da bama zaka ganshi a haka ba. A lokacin da naso in taimaka mishi ai ƙi yayi. Inusa in dai kanaso zumuncinmu yaci gaba, to kar ka sake ka taimaki Gwadabe da sisin kwabo" Sai wani huci yake yi, yana hura hanci. Yaci jar shadda dinkin tazarce, idanunshi cike dam da farin kwalli. Murmushi Gwadabe yayi kawai ya wucesu. Tafiya kawai yake yi, amman baya ma iya ganin gabanshi. Tunanin shi kuwa shine. Anya Babala itace ta tsugunna ta haifeshi kuwa? Anya su Yaya Hambali ƴan uwanshi ne su kuwa? Sai dai yana tuna yanda suka taso cike da kulawar Yaya Hambali, ya kuma haɗe kawunansu duka, cikin soyayya yake musu komai. Har wanka yayi musu da hannunshi. Gashi da yawan taimako, hakannema yasa gashi duk ya jaye ƴan uwan nashi, kuma dukkansu da bazarshi suke taka rawa. Daga sanda ya Auri Iyabo zuwa yanzu yana ganin ƙiyayya. Sun kwana basu ci abinci ba, yaje wajen ƴan uwanshi ya bisu kab aka rasa wanda zai taimaka musu. Hawayene yaji suna zuba a idanunshi shaa. Da sauri ya goge yana dariya kamar mahaukaci. Ko da yayi salllama a gidan Bara'u, Sakina ce ta fito. Tayi mamakin ganin irin ramar da Gwadabe yayi. Bayan sun gaisa ne take cewa. "Gashi yana gona. Amman bari insa Shehu yayo kiranshi. Ka shigo daga tsakar gida" "Nagode Sakina" A sanyaye ya shiga tsakar gidan. Ya zauna akan taburmar daya samu a shimfiɗe a baranda yayi saroro dashi. Ruwa Sakina ta kawo mishi, sai da yasha sannan yace. "Ina yaran ke kaɗaice a gidan?" "Sun tafi makarantar allo dake yau babu boko. Ƴan kuci_kucin kuma Baban ya tafi dasu gona. Ya wajen su Baba Magaji?" Ɗan murmusawa yayi kafin yace. "Kowa yana lafiya, sannu fa da ɗawainiya Sakina allahu ya bar zumunci" Dariya tayi ta miƙe abinti taci gaba da kaye_kayenta har Bara'u yayo sallama ya shigo. Ganin Gwadabe ne yasa yayi Dariya, sai dai ya girgiza da yanayin daya ganshi a ciki, musamman baƙi da ramar da yayi. Ga wani rawani daya tuntuma a kanshi irin na buzaye. "Baƙin buzu gallah mu ka yi a gidan namu, Gwadabe maraba lale" Zama yayi suka tafa. Sakina ta dure musu ɗumemen dambu yaji rama da man shanu. "Fara cin abinci tukunna mu sha labari" Sai da Gwadabe ya ƙoshi ya sha ruwa kana yace. "Na sameku Lafiya ya ɗawainiya?" "Lafiya lau, ɗawainiya ai yiwa kaine Gwadabe. Ya bayan rabuwa?" Ɗan sauke kai ƙasa yayi yana wasa da yatsun ƙafarshi yace. "Sai alkhairi Bara'u. Ya gona?" Dariya yayi yace. "Gona lafiya lau, sai godiyar Allah. Lafiya irin wannan ramar haka Gwadabe, ciwo kayi mu bamu sani ba ko me?" Bara'u ya faɗa cikin kulawa. Ajjiyar zuchiya Gwadabe ya sauke kana yace. "Wallahi babu ciwo yau ce kawai Bara'u. Ga ciwon damuwar rabuwa da iyali lokaci guda shima yana damuna ainun. Kuma sana'ar tamu tana da wahalar gaske" Ajjiyar zuchiya Bara'u shima yayi. "Toh Allah ya kawo maka mafita. Ai rashin iyali ga wanda yasan daɗinsu babban tashin hankali ne. Sannan ya haɗema har da yanayin can ƙasar kasan baka sababa. Amman ya batun aurenka da Shafa da Hadiza?" "To Bara'u ni fa gani nake yi in haƙura da Shafa kawai. Bana jin motsin san su sam a raina. Ganin girman waɗanda suka mun kyautarsu kawai nake ji. Ka ganni sai in yi sati biyu ban riƙe nera biyar tawa ba. Da haka ne zan auri mata biyu? Atampa biyu kawai na iya ajjiyewa da sunan kayan akwati fa. Duk da Tamu zai taimaka mun, amman dole inma Hadiza" Shiru Bara'u yayi yana nazarin maganar Gwadabe, domin maganarshi abun dubawace. "To Gwadabe maganarka gaskiya ce domin Allah. Amman dole a nemi maslaha, kasan Tamu ba lallai yaji daɗi ba. Shafa kuma ta gama sa ranta da kai. A gidansu duk ansan da maganar aurenku fa. Ni ina ganin ka daure dai ka auresu du biyun. Sai a tura bikin ita Shafa zuwa nan da ko shekara ne. In yaso ita Hadizan sai ka soma aurenta. Ko yaya kake gani?" Kai Gwadabe ya gyaɗa kafin yace. "To hakanma gaskiya ne. Nima abinda du ya dameni kenan. Kaga kuwa in da za a ɗaga ɗin zuwa lokacin da ka ambata ɗin da abun zaiyi kyau. Muna sa rai abubbuwa zasu warware da izinin Allah. Dan sana'ar tamu in Allah ya dafa ma mutum yana samun arziki. Da ace ina da wasu jari ma a hannuna da abun sana'a zan dinga tafiya dashi ina ɗan siyarwa haka. A samu ɗan na kashewa." Bara'u yace . "Ga shawara kana ganin in kana siyar da magungunan gargajiya ba zaka samu ciniki ba? Da sai ka jaraba ai, ko maganin dattin ciki, da maganin basir, da ɗan na warware gaɓoɓi da sai ka dinga dafawa kana ƙullawa a leda kana tafiya dashi. Kuma fa akwai riba." Shiru Gwadabe yayi yana nazari kafin yace. "Wannan ma shawarace Bara'u. Sai in jarraba, in zan tafi zan tafi da wasu saƙe saƙin in sha Allah" "Sai kaga Yaya Hambali ya gyare gida ko?" Yayi maganar yana dariya" Gwadabe yace. "Gida yayi kyau sosai Bara'u, sai haska gari yake yi." "Hmmm ai Yaya Hambali in faɗa maka harkace ta buɗe mishi. Wani bawan Allah ne ya bashi kwangilar dabino, da jar dawa ko buhu nawa yakai yana siya. Kai duk inda dabino da jar dawa suke Yaya Hambali siye su yake yi ya kaima mutuminnan. Shi yasa bashi da aiki sai zuwa ƙauyuka ƙauyuka neman jar dawa Ance gidanshi na kano ya rushe ya maisheshi bene. Kuma ya sai gonakai shimfiɗa_shimfiɗa a bayan gidan gonar mai gari baka ga girmansu ba, wai yanaso bana yayi noman jar dawa ne." Gwadabe ya taya ɗan uwan nashi murna sosai. Har cikin ranshi yaji farin ciki, yasan ko babu komai Babala zata huta. "Ni na mance sai kazo kaga Auta a gida miji ya sakota uwar miji ta hanata zaman lafiya " Cikin mamaki Gwadabe yace. "Autan aka saka Bara'u?" Baki Bara'u ya saki yace. "Wai baka ganta a gidan ba, ko dai baka tsaya kayi hira da Babala bane?" "Hmmm Bara'u kenan" Nan ya kwashe duk irin cin kashin da Babala da Yaya Hambali su ka yi mishi. Ya ɗaura da cewa. "Zuchiyata dab take da bugawa. Dame zanji Bara'u . Batun mutuwar auren Auta kuma duk Babala ce ta sa aka sakota, ta hanani zama da Iyabo, gashi uwar miji ta hana Auta zaman aure. Lokuta da dama iyayenmu suna kusa kurai" Tsit Bara'u yayi, idanunshi suka rine da kyar yace. "Hakane Gwadabe kayi haƙuri. Ni kaina Yaya Hambali babu irin cin mutuncin da bai yi mini ba akan sai dai in cire Toye daga boko. Dana faɗa mishi gaskiya kuma yace na zageshi. Gwadabe Babala har gidanmu taje ta kai ƙarana" Sun jima sosai suna tattaunawa. Da rana saiga ƴan makaranta. Toye ya girma abinshi, bai mance da mahaifinshi ba. Har iyabo Toye saida ya tambayi Gwadabe. Zuchiyar Gwadabe sai tayi sanyi jin yaron bai mance shi ba. Sai da daddare Gwadabe ya samu damar yin waya da Hadiza da Shafa.Kwanan Gwadabe biyu a Takai, amman zaman duk ya gundureshi sabida irin hantara da munanan furucin Babala a kanshi. Bayan ya huta sai kuma yabi dangi da gaisuwa gida_gida. Kwananshi Takwas yayi sallama dasu. Dashi da Bara'u suka dunguma Habuja wajen Tamu domin su yi mishi bayani akan batun ɗaga biki. Bayan sunci abinci sun huta. Ya ga ƴan biyu ya basu ƴar tsarabar da yayo musu da yaran Tamu, ganin yanda yaranshi su kai kyau da gani ana kulawa dasu, dan kayan jikinsu ma mai tsada ne. Raɗa yaima Bara'u a kunne yace "Maganar ɗaga bikinnan a barta Bara'u. Kunya duk ta lulluɓeni wallahi, jibi hidimar da yaketa yi da yara fa" Kai Bara'u ya gyaɗa halamar hakane. Fitowar Shafa itace ta dakatar da Tamu da magana dan tambayarsu yake yi gulmar me suke yi. Jus ta dire musu tasha ado tayi kyau tana ta ƙamshin turare me daɗi. Kanta a ƙasa ta gaishesu. Bara'u yace. "Ja ira yau mu ake jin kunya Shafa? Lallai kin girma" Murmushi kawai tayi mishi. Gwadabe sai kallonta yake yi yana murmushi. Tamu ne ya miƙe tsaye tare da cewa.." "Kafin su gama Bara'u tawo mu shiga kaga gari. Ai kwana zaku yi dai ko? Dan nasa Shafa ta gyara muku shago an sa katifa ma" Bara'u ya miƙe tsaye yace. "Kwana zamu yi kai bama ɗaya ba, dan wallahi ni kam saina huta. Kai kaji falonnan wani sanyin fanka kuwa?' Tafawa su kayi tare da ficewa. Fitarsu ce yasa hankalin Gwadabe dawowa gareta, itama saita gyara zamanta. Idanu ya ƙura mata ita kuma sai sinne kanta take yi kunya ta isheta. Shi kuma yau ne ya samu damar kallonta tsab. Yarinyace gaskiya, tana da madaidaicin kyau, da matsakaicin tsayi, bata da diri a kallon da yayi mata a tsaye, amman ƙirjinta a cike yake masha Allah. "Gani a gabanki amman kin kasa cewa dani komai. Ke da kika ce kinata mafarkin zuwan wannan ranar. Sai naga kin kasa cewa komai " Sake sunne kanta tayi ƙasa. Yawan kunyarta sai ya zama silar burgeshi, kunya tana yima ɗiya mace kyau, tana zama wani ado na musamman gareta. Murmushi yayi kawai tare da girgiza kai. Shafa tayi mishi ƙarama sosai shi yama rasa taya zasu yi wannan zance. Da dai taga shirun yayi yawa sai yace. "To a ɗago fuskar mana in ɗan kalla" Ɗagowa tayi ta ɗan kalleshi, shima ya kalleta, tayi saurin kawar da kanta tare da cewa. "Barka da isowa, ya ka baro mutanen Takai?" Sai da ya yi Dariya sosai kana yace. "Suna lafiya, ya karatu ya aikin kuma duk anayi ko?" "Anayi Alhamdulillah" "To Allah yayi jagora. Sannu da ɗawainiya da ƴan biyu. Ayashe ta sanar dani irin hidimar da kike yi dasu. Tamu kuma ya bani labarin irin shaƙuwar dake a tsakaninku. Kina son zaki tafi dasu ne in mu ka yi aure?" Ƙasa tayi da kanta tana wasa da yatsunta tace. "E inaso in tafi dasu, sabida zasu yi maraicina, kuma nima zanyi kewarsu da yawa. Gashi ba ƙasa ɗaya ba balle ince zan dinga sawa a kawo mana su hutu. To Amman Yaya Tamu yace babu wanda zai rabashi da su" Dariya Gwadabe yayi. Dariyar yadda take magana muryarta na rawa kamar tana gaban dodo." "Zan mishi magana in lokacin yayi. Dan inason in haɗe kan yarana. Toye dake wajen Bara'u ma zan ɗaukeshi in yaso sai in ba yayarki tayi riƙonshi. Zanfi samun nutsuwa" Da sauri ta ɗago tace. "Wacece Yayata kuma?" Kallonta yayi yana nazarinta, a muryarta yaji kishi. Sai ya basar yace. "Hadiza nake nufi ƴar uwata wacce zan haɗaku" A sanyaye tace. "Ka yanke hukuncin soma aurenta kafin ni kenan? Bayan ni aka soma baka kafin ita" jin furucinta da rawar muryarta sai yasa yaji kunya. Ba shiri yace. "Ko ɗaya Allah shine masanin wacece zata zama fari, in Allah yaso sai kiga rana ɗaya an ɗaura auren. Nace yayarki ne sabida Hadiza ta girmeki sosai. Bazawarace yaranta biyu" Ɗan boyayyen ajjiyar zuchiya ta sauke. A haka hirar taci gaba da gudana. Tsarabarta ya miƙa mata, ya miƙo mata agogon da Hadiza ta bayar a kawo mata. Har a fuskarta taji daɗin kyautar Hadiza sosai. Miƙewa Gwadabe yayi tsaye yace da'ita zashi masallaci an soma kiran sallar la'asar. Haka dai Gwadabe suka kwana biyu a gidan Tamu. Sunga karramawa sosai. Ranar juma'a ya kama hanyar nijer, Bara'u kuma ya kama hanyar Takai. IYABO. Tsarki ya tabbata ga Allah mai kowa mai komai. Sarkin dake da iko a kan kowa da komai. Muna zazzaune mata da maza sai shigowa suke ta faman yi. Fuskokin al'ummar cikin wannan jirgi mafiya yawansu cike take da annuri. Barinma ire_irenmu da bamu taɓa tunanin samun irin wannan damar ba ko a mafarki. Wata na'urace muka ciyo tana magana da turanci akan kowa ya ɗaura belt ɗinshi ya gyara zama zuwa minti sha biyar jirgi zai tashi. Ma'aikatan dake cikin jirgin sun taimaka mana ainun. Dan daga ni har Uwani bamu iya saka wannan bel na jikin kujera ba. Mintunan da wannan na'ura na cika jirgi ya soma tafiya da tayoyinshi a cikin filin girji. A hankali _a hankali har jirgi ya tashi sama. Sai da ya tsayu a sama kana na dawo cikin hayyacina dan juwa naji inaji harda hararwa. Wasu tsofaffi ma harda ihu dan tsoro. Taga na kalla na ganni a cikin gajimare. Gurun da Yaya Hamma ya bani na sake matsewa a hannuna na lumshe idanuna, abubbuwa ne suka haɗemun. Murna da kuma alhinin barin Dada. Da kuma damuwa da fargabar rashin furta mun kalmar soyayya da Yaya Hamma bai yi ba. Ta wani ɓangaren gani nake yi na rasa shima, musamman inna tuno da irin soyayyar da Daso take gwada mai. Bani da masaniyar sanda zuchiyata ta kamu da soyayyar Yaya Hamma. Ada nayi tunanin damuwa da lamarina shi ya haifarma da zuchiyata shaƙuwa dashi. Ayau rabuwarmu na sake samun yaƙinin motsin sone a ƙirjina bana shaƙuwa ba. Kuma a yaune na tabbatar da soyayyar da Yaya Hamma ya ke yi mini. Iska na furzar daga bakina. Idanu na sake lumshewa. Allah sarki Gwadabe yanzu inaji ina gani ni Iyabo na rasaka, dole in yi aure in hayayyafa da wani ɗa namiji bayanka. Ji nayi Uwani ta balbalin ta dafani. Juyowa nayi na dubeta, murmushi tayi mun, nima shi na mayar mata. "Iyabo, ko Hamma bai faɗa ba tsananin sonki yake yi sosai. Ki duba har kwalla sai da ya zubar, banda irin ɗawainiya da kulawar da yaita baki. Ya kamata ki kwantar da hankalinki dan nasan zuchiyarki bata iya kamuwa da soyayya ba. Sannan ki bari ki samu nutsuwa kiyi tunani akan wannan soyayyar. Ki sani dai Hamma a ruga yake rayuwa ba'a birni ba, nifa banga dalilin ma da zaki yi sake har zuchiyarki ta kamu da sonshi ba kema. Na fa yaba ma ƙoƙarinshi gaya, amman baima dace batun wani so ko aure ya ɓullo ba" Mrs Bukhari *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* [8/12, 5:09 PM] +234 803 635 0240: NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BOOK 2 7 Ajjiyar zuchiya na sauke. Uwani duk abinda kika faɗa gaskiya ne akan Yaya Hamma. Amman a jikina gani nake yi tunda bai furta mun kalmar soyayya ba har mu kai bankwana, to bazai furta mun ba. Kar ki manta kasarfa zamu bari, tunda muka shigo garin Kano ya dace ya fallasamun asirin zuchiyarshi ko?" Dariya Uwani tayi mun. "Iyabo manya. Maganarki haka take. Amman in kin lura Hamma baƙauyene cikakke, babu wayewa a tattare dashi. Ni nafi tunanin ya rasa ta yanda zai furta miki kalmar so ne. Amman a shawarce kar ki bari zuchiyarki tayi zurfi a soyayyar Hamma. Kar mu dawo kiga saɓanin abinda kike tunani azo a samu matsala. Shekara uku ba kwana uku bane. Kuma ƙila mu wuce tsawon wannan shekarun." Haka mu kaita tattauna zantuka ni da Uwani. Dare ya ratsa sararin samaniya sosai. Ma'aikatan cikin jirginne suka soma rabon ruwa da lemo, da soyayyen cincin, da naman kaza. Sai shillawa muke cikin gajimare. Awannmu 6 da minti ashirin muka ji jirginmu ya sauka. Dukkanmu muka cika da murna a tunaninmu mun iso Makka ne ashe ba haka bane, itofiya muka iso. Hajiya Salamatu ta sanar damu zamu kwana a Airport zuwa gobe jirginmu da zai ƙarasa damu saudiyya zai zo. Ta ɗaura da cewa. "Ni daga nan shine iyakata daku. In kuka sauka a Makka Hajiya Mangala zata turo duk a ɗauke ku. Allah ya ba da sa'ar abinda aka fito nema." Daga nan muka ɗunguma inda zamu kwana. Anan muka rarrama sallolin da ake binmu a filin Allah. Washe gari duku_duku jirgin da zai mayar da Hajiya Salamatu zuwa Najeriya ya tashi dasu, cike da fasinjojin Najeriya. Mu kuwa a gantale ga baƙar yinwa haka mu kai ta zama a wannan fili. Gashi cikinmu babu wacce take da kuɗi, ruwa ma sai da mu ka roƙa aka bamu, shima wasu basu samu ba. Sai kusan magriba aka sanar mana jirginmu yazo. A madadin Makka, sai akace ai dama Riyahd za'a kaimu. Haka aka ɗuramu a jirgi. Daga itofiya zuwa Riyahd Awa 2 da minti hamsin da huɗu ne ya kaimu. Aka sauke mu a filin jirgin. King khalid international airport. Tun daga sakkowarmu jikina ya mutu. Bani kaɗaiba duk tawagarmu jikinsu duk a mugun mace. Bayan mun je ɗakin ɗaukar jaka, daga nan aka nuna mana ƙofar fita, duk muka fito yu. Titine shimfiɗaɗɗe, sai tsirarin motoci masu shige da fice jefi, jefi. Ga wutacen lantarki masu haske kamar rana. Dan ko allurarkace ta faɗi zaka ganta kamar ba dare ba. Wata farar Hajiya ce ta nufomu tana murmushi, tasha gwala_gwalai haƙorin makka har guda shidda ne reras a bakinta. Da isowarta sai muka ji tayi Hausa raɗau. "Kune mutanen Hajiya Salamatu kano to jidda?" Kusan dukkanmu muka haɗa bakin wajen amsa mata da. "E mune Hajiya" Dariya tayi tace. "Masha Allah komai yayi kalas. Yalla ga mota bus ku shiga muje" mota muka shisshiga kowa ya zauna, iyakar galabaita dai munyi. Yinwa kuwa ba a maganarta. "Uwani nifa jikina ya mutu tunda akace Riyahd za a kawo mu. Domin ba haka mu ka yi da Hajiya Salamatu ba." Buɗar bakin Uwani tace. "Karma kiji komai Iyabo da Makka da Riyahd duk abu ɗaya ne. Kuma ƙila tana nufin a makka za a sama mana aikin wanke_wanken tunda mu ba zama mu ka zo yi ba." Sai data faɗi haka sai na ɗanji sanyi. Duk da dai zuchiyata a cike take da tsoro ainun. Tafiya kuwa tun anayin ta marmari, har abun yazo ya gunduremu, tun cikin dare muke sharara gudu bamu muka isa inda zamu je ba sai da asuba. A ƙofar wani babban gidan bene motarmu ta tsaya. Muka sassauko kowa a wahale, wasu tsofaffi daga cikinmu sai taimaka musu muka yi suka fito tsabar jigata duk sunyi fitsari a jiki. Hajiya Mangala ce ta fito daga cikin motar ta ta nufomu. "Yalla muje ciki, kun sha hanya, a yi wanka a karya sai kowacce ta kwanta ta huta kuma" A baya muka bita zuwa cikin gidannan. Ko wacce na faman tiri_tiri da kaya. Ni da Uwani ne kaɗai bamu da wasu wadatattun kaya, a jaka ɗaya ma muka haɗe kayan. A bene na shida muka tsaya. Mu dai duk inda Hajiya Mangala ta ɗaga ƙafarta anan muke sa tamu ƙafar. Wasu ɗakuna ne a jejjere reras a wani dogon falo, ko wacce ƙofa da number a jiki. Ɗaki na ashirin daga nan ta soma. "Mutum goma goma zaku shisshiga, daga wannan ɗakin zuwa har inda zai isheku. Amman wannan me lamba ashirin ɗin mutum biyu ake bukata. Ke da ke ku shiga nan tunda kune a tsaye a wajen." Ta nuna ni ni da Uwani muna tsaye riƙe gam da hannun juna. "Amman kafinnan ko wacce ta bani fasfo ɗinta da wayar salula in tana dashi. Ko wanne ɗaki akwai land line da zaku kira ƴan uwanku na Najeriya." Nan Uwani ta zaro wayarta ta miƙa, muka haɗe fasfo muka bata, na sanar mata bani da waya. Duk da haka sai da tasa wata mace ta caje kayanmu, ta caje jikinmu, hannunta har cikin wando, har ƙasan mama sai da ta ɗaga, da gashin kai. Tana gamawa damu muka shige wannan ɗaki da sallamarmu. Wallahi Allah sai da gabana ya yanke ya faɗi. Siririn gaske ne ɗakin, iyakar tsayin katifa, babu masaka tsinke. Ga mata nan su takwas a kwance ko wacce a karamar katifa irinta ƴan makaranta. Ragowar katifu biyun kuma jakunkuna ne akai a jibge. Daga bakin ƙofarnan da yake da ɗan sararin da muke tsaye, babu inda zamu ɗaga ƙafarmu mu ajjiyeta sai dai a katifar mutane. "Uwani na shiga uku, kinga wani ɗaki kamar kwanciyar kabari. Kafin uwani tayi magana aka buɗe ɗakin. Wannan matar data caje mu ce. "Dama nasan za'a rina wai an saci zanin mahaukaciya. Ke Ƴar ɗas, ƴar ɗas kina jina fa" Wacce aka kira da ƴar ɗas ta tashi zaune tana miƙa. Ni dai in ba gizo idanuna yake yi mini ba sai naga kamar namiji, akwai dai gashi a kanshi, amma ƙirjinshi babu komai a shafe, duk da akwai ƙunƙumar macce wacce bata da nono, kuma macece, inta haifu sai kan nono ya bulloƙo ta shayar da jaririn, to ina tunanin ko Ƴar Ɗas ƙunƙumace. "Oh ma'aikin Allah na Madina ni Ƴar Ɗas. Yanzu Taraliya duk illahirin jama'ar dake ɗakinnan saini kika ga damar tasa, sabida riƙaƙƙem iskanci? To gani gani" Magana take yi da lanƙwasa, gata da yanga" Wacce ta kira da Taraliya tace. "Baƙi mu ka samu, kisa waɗancan matan su kwashe kayansu a kafinsu, zasu kwanta su huta" Ƴar Ɗas tai mana kallon uku saura kwata tace. "Bayin Allah maraba da zuwa. Ke waccan tsalllako ga katifa can. Kiyi watsin ruwan tsarki da kayan da kika gani a katifar. Ke kuma ga bayan gidaa bayanki, faɗa ki shilla wanka, inba haka ba zafi ne zai kasheku" Dariya Taraliya ta saka tace. "Baki da dama yar Ɗas" Itama dariyar tayi tace. "To ai gani suke daɗi muke ji in mun baro gida Najeriya. Tunda sun shigo sai du a haɗu aci wuyar tare ai. Duk wacce ta kwace ta tafi Najeriya ta ba da labari" Take naji wani zum_zum. Tsoro ya kuma shigata. Ina tsaye Uwani ta shiga tsallake matan dake kwance. Aiko ta faɗi akan wata mace tim, ga uwani ba kaɗan ba. Matarnan ta saka ihu da kururuwa. "Haba baiwar Allah wannan ai iskanci ne, ji yanda kika faɗo mun so kike ki karyani?" Cike da fitsara take maganar gata yarinya ƙarama. Kiyi haƙuri baiwar Allah " Na faɗa ina daga tsaye. Ta bani amsa da cewa. "Babu komai. Sannunku da zuwa baƙi" Da ƙyar Uwani ta yinƙura da rarrafe ta isa waɗannan katifun biyu ta ajjiye jakar kayanmu ta zauna. Ƴar Ɗas ta dubeni tace. "Wannan tsaiwar ta babu gaira babu dalili dame yayi kama. Kin zo kin tsaya mun a ka, sai in tayar miki da aljanu Allah. " A tsorace na shige ƙofar dake kusa dani. Wani bayan gidane tsukukun gaske, komai dai tsab, ga ruwa a fanfo ga bokiti. Tuɓewa nayi na shesshiƙama jikina ruwan sanyi, dan a jiƙe kayana suke da sufa sharkab. Jiri da ciwon kai na yinwa duk yabi ya addabeni. Alwala na ɗauro na fito kayan dana cire su na mayar na saka hijabina na fito. Ƴar Ɗas tana zaune tana kallon ƙaramin mudubi na hannu. Uwani tsallako kije kiyo wankan" Uwani da tayi jigum tace. "Faɗuwa zanyi matsawar ban saka abinci a cikina ba. Bani da nutsuwar wanka, ki ƙyaleni kawai" Kai na girgiza dan nima yinwar shirin kayar dani take yi. Kafin ince wani Abun sai ga Taraliya ta buɗe ƙofa ta miƙo mun gurasa guda huɗu a hannu, da wani romon miya. Nasa hannu na karɓa ina jujjuya abincin. "Ku biyu ke da abokiyar tafiyarki. Ku yi da jiki maza, zaku fita yanzu da Hajiya Babba" Danƙarewa nayi a tsaye mamaki na neman ruguza nutsuwata. Da ƙyar naja ƙafata na tsalllaka na samu uwani. Loma shida gurasarnan tayi mun. Jima nayi kamar yinwar na sake tsokanowa wallahi gashi ko ruwa ba'a bamu ba. Sai Ƴar Ɗas muka roƙa ta bamu gora ɗaya ƙarama. Uwani daure ki je ki watso ruwa, ana binmu sallah fa, kuma kinga ance zamu fita." Uwani dai bata ce komai ba ta tsallake matan dake ta bacci hankali wance. Ƴar Ɗas dan Allah inane gabas, sannan a ina zanyi Sallah?" A yangance Ƴar Ɗas ta ce. "Ga gabas kin ganta. Batun inda zaki yi sallah kuma katifarki zaki jingine a bango kiyi sallah. In baki da dadduma sai ki shimfiɗa ɗankwalinki" Harna rama sallolin da ake bina hawaye bai dena zuba a idanuna ba, zuchiyata ta karaya ina hango mana wahala da wulaƙanci a gabanmu. Uwani itama katifar ta gingine ta soma rama sallolinta. Bata kai ga gamawa ba Taraliya ta leƙo kiranmu. Uwani bata idar da sallah ba Taraliya" "Tayi sauri ta sallame, dan Hajiya Babba ba'a ɓata mata lokaci. In ranta ya ɓaci baku ba cin abincin rana a cikin gidannan" Uwani tayi Sallama, ta dubi Taraliya tace. "Akwai sallar isha a kaina ban rama ba fa" Ƴar Ɗas tace. "Shawara ki tashi kuje, in kun dawo kya rama. Ba a yin musu da duk umarni. Ke wata rana ma kina ganin lokacin Allah zai shiga ya fice baki yita ba. Wata rana ma sai dai ki rama sallolin cikin dare a kulle a ɗakin da aka baki a matsayinki na ƴar aiki." Jikinmu na rawa cike da tsoro da tsinkewar zuchiya muka fice a ɗakin, kayanmu da jika. Haka aka turbutsamu a mota, wasu akan cinyar wasu. Duk wanda na kalla sai inga tana share hawaye, imma da mayafinta, imma da gefen zaninta. Zukata sun shiga damuwa da ruɗu. Wani gida aka kaimu, akaita mana aune, aune, bamu muka gama ba sai yamma lis. Basu bamu abinci ba, an dai raba mana ruwa munsha. Ɗakinmu muka tura muka shiga. Babu kowa a ɗakin, katifun dukka suna jingine a bango. Durƙushewa nayi ƙasa na sau kuka mai tsuma zuchiya da gangar jiki. Uwani na jan majina tasa hannu bibbiyu ta ɗago ni. "Iyabo tun a itofiya jikina ya mutu. Amman sai ƙara sama mana ƙarfin guiwa nake yi. Hankalina bai kai ƙololuwar tashi ba sai da muka shigo ɗakinnan mai kama da kabari. Muna cikin tsaka mai wuya a ƙasar da ba uwa ba uba, ba dangi." Kukane yaci ƙarfinta. Uwani mu dokara ga Allah. Allah ya ga xuchiyarmu mu neman kuɗi muka zo yi. Amman na fahimci kamar bayi haka aka ɗauke mu. Shawarar da zan baki, mu kai kukanmu ga Allah kawai. Da zamu samu hanyar komawa gida Najeriya ma da mun koma" Taraliya ce ta turo ƙofa, hannunta riƙe da gurasa kamar dai irin wadda aka saukemu da'ita. "To Wallahi kar ku sake ku sake ambaton Najeriya ma. In kuka kuskura wannan kalmar ta shiga kunne abokan zamanku, zasu isarma da Hajiya Babba. Ba zaku ji da daɗi ba. Sannan ku dena damun kan ku, ku da za'a tura gidan aiki. A can ɗaki sukutum za'a baku ku kaɗai a ciki. Kuma sai abinda kuke son ci zaku ci. Wannan zaman na ɗan lokaci ne. Ku dai Allah ya taimakeku ku samu shigewa da wuri. Dan naji Hajiya Babba na maganar gobe za'a soma raba ƴan aiki. Ku zauna kuci abincinku." Godiya Uwani tayi mata, har zata fita uwani tace. "Wai irin abincinnan kullum ake ci ne? Sannan wannan yayi mana kaɗan mu biyu" Dariya tayi bata ce uffan ba ta fice ta barmu a tsaye jigum. Jiki a saɓule muka rama sallolin da ake binmu. Muka lasa wannan abinci dan sai dai a kirashi da lasawa kawai. Muna zaune kowa dai da tunanin daya addabi zuchiyarshi. Yaya Hamma ne ya faɗo mun, dole na ɗan murmusa harma naji kwaranyar wani ruwa mai sanyi a zuchiyata. "Uwani ya kamata mu tambayi land line ɗin da akace akwai a ko wanne ɗakin ai. Ko dan ki samu ki kira mijinki ki sanar mishi isowarmu ko? Nima inason in kira Burodami in sanar musu da saukarmu" "Hmmm Iyabo mu nutsa mu gane kan gidan tukunna, kinganni yanzu haka yinwa kamar zata kasheni wallahi, gashi jikina ko ina ciwo yake yi mun kwanciya zanyi ko zan iya runtsawa a wannan halin da muke" Katifarta ta yar, ta ɗaura jakar kayanmu a katifarta, dan babu waje, kowa da kayanshi yake matashin kai. Ni dai ina zaune in tuno Dada, in Tuno Gwadabe, in tuno Ƴaƴana, in tuno Yaya Hamma da kuma Daso data haɗa zuchiyata da fargaba. A wajen a zaune bacci ya kwasheni ban sani ba kasancewar jikinmu a nune yake sosai, ga yinwa sai ta galabaitar dani. Allah cikin ikonshi sai da Asuba na farka, a ƙasa na kwana abina. Matan ɗakin namu wasu na kwance sunata baccinsu, yayinda wasu kuma suke Sallah, cikin masu Sallah harda Ƴar Ɗas, abunda ya bani mamaki shine banga Ƴar Ɗas da mayafi ko hijabin Sallah ba, banga kuma wannan yala_yalan gashin dana gani a kanta jiya ba, sai suma irin ta maza. Da Ɗan daudu muka kwana muka tashi ni Iyabo?" Na furta a zuchiyata ina mamaki, raɓewa nayi ta bayanshi na wuce zuwa toilet na ɗauro alwala. Ni dai har na idar da sallah ban dena mamakin Ƴar Ɗas ba. Sai hirarta take yi da mata ana tafawa, gata da barkwanci sosai. Ni dai naga matan ɗakin daga wannan mu ganta ta shigo da tea da biredinta, sai muga masu kaza gashasshiya, da masu wata doguwar shinkafa wacce ni tunda uwata ta haifeni banga shinkafa da kyau da tsarin wannan shinkafa ba, gashi taji naman kaza, ƙila itace shinkafa kaza da muke jin labari. "Bayin Allah ni ban gane ba tambaya ce dani dan Allah" Cewar Uwani data tashi tsaye. Ƴar Ɗas ta mike ƙugu a hannu yace. "Na taɓoki da alheri wai kishiya ta taɓa kishiya da bakin wuta. Faɗi tambayarki in rabtaɓo miki amsa, dan dana ɗumama cikina da kaza da laban kwanciya zanyi sai azahar kuma" Uwani tace. "Mu tunda muka zo wata bushasshiyar gurasace ake bamu, da wani romo da bamu san na meye ba. Bugu da ƙari ma ba isarmu yake yi ba. To sai kuma naga ku ko wacce da abinda ta saka a gaba tana ci, muna son ƙarin bayani." Ni kaina da Uwani bata yi musu wannan tambayarba, da ni zanyi musu. Yinwa tana addabarmu ainun, har ƙirjina ya soma nauyi. Ƴar Ɗas ya doki cinyarshi yayi juyi da ihu kafin yace. "Wannan gurasa da romo duk muma mun cita kafin mu yage rigar bauta, mu sa ta ƴanci. Duk wannan kayan ci na albarka da kike ji da gani, ko wacce da guminta na halak ta siya. In baki da kuɗi cin gurasa dole, batun ƙoshi kuwa kima fita zancan wannan. Kuma anan ba mai taimako wani, ko wacce ƙasarta ta baro ta fito biɗar kuɗin halak" Ɗayar matar mai Suna Madina ta dubemu ta ɗaura mana da cewa. "Idan kuka ƙara haƙuri da sannu komai zai wuce muku. Wuyarta ku soma aiki, kuɗi kam sai dai ku tura gida ma, abinci sai kun ture. Kunga irin baƙar azabar ni dana sha kafin in samu gidan aiki? Hmm abun yana da munin da ina faɗa muku zai karya muku zuchiya. Ku dai kuyi ta yin adda'a shine kawai" Taraliya ce ta miƙo mana wannan gurasa ta masifa. Sai dai yau matan ɗakinmu sun taimaka mana anyi mana karo_karo na abinci shine muka samu muka ji dama_dama. A taƙaice dai munfi kwana goma muna zaman jiran a kaimu gidan aiki. Anata ɗauki ɗaɗɗaya. Uwani da ƙyar ta samu lambar hajiyarsu ta shiga ta sanar da'ita isowarmu, sai ranar hankulansu suka kwanta da suka ji muna cikin ƙoshin lafiya,. A ranar aka tafi da Uwani gidan aiki, ranar nayi kuka kamar raina zai fita. Itama tana wannan kukan aka fita da'ita. Ni kaɗai na wuni ƙwalam a ɗaki, sai da nayi la'asar ne na shiga ɗakin dake jikin namu na tarad da su Hadiza suna ɗaki suma a zaune suna ɗan taɓa hira a tsakaninsu. "Iyabo kin leƙo ne, ina Uwani na ganoki ke kaɗai?" Cewar Hadiza. Tare da'ita muka tawo daga Kano. Sai da na zauna kana nace. Uwani ta tafi gidan aiki Hadiza" "To nayi mata barka wallahi muma nan duk zaman jiran hakan muke yi. Duk da ance aikin gidan larabawa ba ƙaramin aiki bane na azaba. Wasu fa wai har dukansu akeyi a gidan aikin." Idanu na zaro nace. "Yanzu Hadiza da girmanmu sai a kamamu da duka?" Dariya ma maganata taba ƴan dakin. Hadiza tace. "Hmmm Dattijuwar da take bamu wannan labarin kinga fa katifarta" Ta nuna mun katifarta a jingine" "Har bayanta ta nuna mana duk shatin bulala. Wannan dalilin ne yasa ta baro gidan aiki tana buƙatar a sauya mata gidan aiki. Duk matan dake cikin ɗakin ku fa da yawansu matsala suka samu a gidan aiki shi yasa kika gansu, za a nema musu gidan aikine" Ni dai jikina du yayi sanyi sosai. Na dubi Hadiza nace. In babu damuwa zan dawo ɗakinku Hadiza, can ɗakin namu basa zama, in suka fita sai dare, wasu ma sai su kwana biyu basu dawo ba" "Jeki maza ki ɗakko kayanki kinji, ai sai abun yayi miki yawa." A ɗakin su Hadiza kwanana biyar. Naji labarai masu tayar da hankali, da irin matsalolin da baƙaƙenmu suke fuskanta a gidajen aiki iri daban_daban kuma masu haɗarin gaske. Nifa tun daga Itofiya na soma ɗan daka ce ban baro ƙasara Najeriya ba. A ranar dana cika kwana goma a ɗakin su Hadiza nima akace in haɗo kayana waɗanda zasu ɗaukeni aiki zasu tafi dani. Hawaye na soma zubarwa da girmana, na suri ledar kayana, duban su Hadiza nayi da muka shaƙu a kwanaki gomannan nace. Allah ya sake sada fuskokinmu da Alkhairi, ni na tafi, ku taya ni da adda'a nima zan dinga yi muku" Ina kaiwa nan Taraliya ta figi hannuna zuwa wajen mota. Wata balarabiya da mijinta na gani a gaban mota, ni kuma Taraliya ta dannani a gidan baya. Motarnan na soma tafiya na runtse idanuna hawaye sai kwaranya yake yi a idanuna. Tafiya muka yi mai yawan gaske zuwa wani garin kuma. A cikin katafen wani ƙerarren gida motar ta tsaya. Ni dai ganin sun fito, nima saina ɓalle murfin motar na fito. Balarabiyar ta dubeni tace dani. "Yalla" Zungui_zungui dai haka naita binta a baya. Muka shiga wani ƙatoton falon da ko a mafarki ban taɓa ganin irinshi ba. Garjejen falone jere da wasu jajayen kujeru marasa ƙafa, duk da na kasa tantance kujerune ko fululluka manya aka jejjera oho. Duk girman falonnan kafet ne mamala a ciki, ga taushi, falon sanyi da ƙamshi yake fitarwa, ga matattakalar hawa bene daga can gefe, ga ɗakuna kusan goma a cikin falon. Ni dai ina biye da'ita zuwa wani ƙaramin ɗaki dage jikin matattakalar hawa bene daga ƙarƙashi haka. Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin tayi, da sauri wata dattijuwa baƙar fata ta buɗe, sai na ganta da atampa a jikinta, kuma tayi mun kama da Bahaushiya. Da larabci wannan balarabiyar tayi mata magana tana nunani halamar dai bayani take yi mata a kaina. Tana gamawa ta haura sama abinta. Wannan Dattijuwar tace.."Sannu baiwar Allah, da ganinki ƴar ƙasata Najeriya ce ko?" Tana faɗar haka saina fashe da kuka. Hannu tasa ta jawo ni cikin ƙaramin ɗakin. Mai ɗauke da gado mai hawa biyu, da katifa a jingine a gefe, sai tulin kayan sawa. A bakin gado ta zaunar dani tace. "Ki dena kuka yarinya. In dai arziki kika fito nema da guminki kin samu. Dan ana biya sosai a gidannan. Amman fa akwai aiki masu yawa sai kinji kamar zaki mutu. Bayana, ƙirjina duk ciwo suke yi mun. Aikin ya gagareni shine naima Hajiyar gidan magana inason zan koma Najeriya a samo wacce zata zama madadina. To gashi Allah ya kawo ki. Zan zauna dake na kwana bakwai in kula dake har sai kin gaggane aikin sai in tafi. Akwai wata yarinya itama aiki take yi da ɗayan shashin na gidannan. Amman ita bata jin Hausa daga wata ƙasar take. Yanzu bari in baki tea da biredi ki ci, sai in zaga dake ki kama aikin ki. Sunana Takarofi" Kukana na share, nace da ita. Sunana Iyabo" "Ayya beyerabiya ce ke ashe? Amman kinji Hausa sosai. Ina zuwa to" Fita tayi tana ɗingisawa, nabi bayanta cike da tausayawa sosai da ido. Bata fi minti goma ba sai gata niƙi_niƙi da kayan karyawa. Lafiyayyen biredi da kakkauran tea har da bota da wainar ƙwai. Cin haɗama nayi ma biredinnan. Takarofi sai kallona take yi. Bayan na kammala tsab sai tace in biyota muje. Nan ta zaga dani lungu da saƙo na gidan, da duk wani aiki da zan dinga gabatarwa. Time table na abinci ta nuna mun gasunan a rubuce reras da turanci. Ko wacce rana da irin abincin da za'a dafa. Cikin sarewa nace. Wai Mama dukka aikinnan ke kike yinsu ke kaɗai?" Murmushi tayi tace. "Shekarata biyar cib a gidannan ina aikin bauta. Ciwon baya, ciwon ƙafa da ciwon sanyi duk sun kashe mun jiki. Aiki zaki zage kiyi KAN JIKI KAN ƘARFI dan basa son saiɓi sai yanzu su koreki." Ajjiyar zuchiya na sauke, na shiga ruɗu da tashin hankali sosai. Nayi dana sanin baro ƙasata nace Kuma tsawon awa nawa kike ɗauka kafin ki kammala aikinnan har ki samu ki huta?" Dariya sosai wannan karon tambayata ta bata. Mrs Bukhari *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu*[8/14, 7:34 PM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 9 "E ya sani, harma ya bani kuɗaɗe yace inna tafi kar in dawo dan in matarshi ta fahimci shi yaimun ciki zata kashemu dukka" Dariya Hajiya Babba ta kwashe dashi ta ɗauki waya ta daddanna, jim kaɗan ta soma larabci tana faɗa ta inda take shiga ba tanan take fita ba. Ajjiye wayar tayi tana tsaki. "Ku tashi ku bani waje, yace zai kawo miki maganin zubar da cikin zuwa gobe. Sai ki zauna da shirinki. Ke kuma zan duba lamarinki, ku tashi kuje" Ni na tallafama Uwani ta miƙe jikkunanmu a mugun mace, haka wunin wannan ranar ya kasance mana cikin tubka da warwarar al'amura. Yaya Hamma na tuno da irin kishinshi. Take na lumshe idanuna hawaye suka gangaro mun. Yarana na kuma tunowa da ubansu. Take murmushi ya suɓuce mun. Takaddar da Khalifa ya bani na ciro a ledar kayana na farketa. Kuɗine sababbi suka zubo masu yawa a mimmiƙe. Uwani ta dubeni tace. "Wannan kuɗaɗen fa Iyabo?" Hmmm Saurayin da nake faɗa miki Khalifa na gidan da nake shine ya bani da suka saukeni a ƙofar gidannan. Uwani baki bani labarin wuyar aikin gidan larabawa ba." Ɗan murmushin dole tayi mun tace. "Sawun giwa ne ya take na raƙumi. Amman duk wata azaba ta tabbata a aiki a gidan larabawa. Wuni guda cur mutum a tsaye kamar jaki. Sallah ma sai kayi da gaske kake ƙwacewa kayi. Iyabo abun babu sauƙi ni duk ƙasar ta isheni gida nake son komawa. Hafizu kuma baya nan yana can Canada ko a wanne irin hali yake sai Allah. Dan ba mui waya dashi ba hajiyarmu ce take faɗa mun. Sai hankalina ya koma gida. Ya kamata ki kira Burodami Debisi kema ai." Baki na taɓe nace. Wannan rayuwa cike take da ƙalubale Uwani. Sai yanzu nake dana sanin ƙin bin shawarar Yaya Hamma da Burodami. Yaya Hamma har shanu ya siyar ya bani jari in dinga zuwa kano ina sare_sare amman wallahi naƙi fur, sabida ni manyan kuɗi nake hari. Uwani shekara na zagayowa ni dai zan tafi gida magana ta gaskiya, da dai na samu ƴan kuɗaɗen juya kasuwanci, da ɗan kuɗin da zan saima Dada ɗan gidan da zata zauna shikenan ni daman ba wani abun nake nema ba. Bani number Burodami in kira ko zan sameshi" Jakarta ta buɗe na hango kuɗi sosai a saman jakar, takaddar da na rubuta lambar ta miƙo mun, na daddana number, na kira ta ƙaraci ringing babu wanda ya ɗaga, na sake gwadawa bata sauya zane ba. Anƙi ɗaga wayar Uwani, zuwa gobe na sake gwadawa . Washe gari da safe muna kan karyawa sai hira aketayi a ɗakin. P.a ce ta leƙo tai kiranmu baki ɗaya ni da Uwani. "Tashi muje Iyabo. Kinsan halin almurar matarnan bata da daɗi sam." Tashi nayi ina lashe hannuna muka je muka sameta da wani mutumi a zaune a kujera. Ashe shine wanda yaima Uwani ciki. Magani Hajiya Babba ta miƙo ma Uwani a farar leda. Jikinta na rawa ta amsa. "Ga maganinan na zubar da ciki. Ɗaya zaki sha, sai ki tura biyu gabanki. Ki jirayi zubar jini minti talatin da sha. Sannan ya bada kuɗi wanda har yafi ƙarfin kuɗin da nake binku ke da ƴar uwarki. Amman ki sani sisin kwabo ba zaki gani ba, wanda ya baki ma in kika bani haɗawa zanyi in karɓe. Ku shirya Zan mai da ku Jidda kuci gaba da zama. Dan yana buƙatar kiyi nesa da garin da yake, dake da wanda ma ya sanki. Dan haka kuje ku ɗebo kayanku yanzu mu wuce, kamfani bata binku ko sisi, sai kuje ku nemi kuɗi a Jidda." Kasa magana mu ka yi dan takaici, da mamakin zalunci irinna Hajiya Babba. Haka muka ɗakko kayanmu, mu kai Sallama dasu Hadiza, nan muka kama hanyar Jidda. A wannan gida na Jidda anan muka ga abubbuwa na tashin hankali, anan muka ga masu ciki iri daban daban. Yaranmu sun zama wasu ƙananun ƴan iska, yarinya ƙarama da buɗaɗɗen idanu. Sai girke_girke wasu daga cikinsu suke ta faman yi. Abun mamakin ma abincin gida Najeriya suke dafawa, dangin dambu, shinkafa da wake. Can gefe kuma ga wasu tsofaffin mata sai ƙulla gyaɗa soyayya da aya suke yi. Sai yima Hajiya Babba sannu da zuwa suke yi. Ni dai ina riƙe da hannun uwani dam. Duk inda Hajiya Babba ta cire ƙafa anan muke ɗora tamu har zuwa wani ɗaki mai cike da kayan more rayuwa. Sai wasu dilolin kaya a zube a tsakar ɗakin da halama na siyarwane. Wata tsohuwar ƴar duniya muka tarar a kwance tana waya sai zabga larabci take yi tana dariya. Bayan ta ajjiye wayar ta dubi Hajiya Babba tace. "Waɗannan sune matan da kika ce zaki kawo ɗin" Hajiya Babba tace. "Gasunan kin gansu. Duk abinda kike ganin ya dace a kansu ki zartar kawai. Kinga me juna biyun ita dai za a iya jefata a kasuwanci dan Abu Khadija ya faɗamun ya bata wadatattun kuɗin da zata lura da lafiyarta. Ita waccan ko gidan aiki ne sai ki jefata, Allah bashi in ta tara kuɗinta ko kasuwancin tura kaya Najeriya ne sai ta soma itama. Tunda dai sun biya kamfani kuɗinta. Ga fasfo ɗinsu nan" Ta zuge jakarta ta ciro ta miƙa ma wannan mata. Kallonmu tayi tace. "Ke me juna biyu, kina da sha'awar kasuwancin tura gumama gida Najeriya ire iren dogayen riguna haka?" Ta nuna mata na zube a tsakar ɗakin. Kana ta ɗaura da cewa. "Harkace mai riba sosai, domin a Najeriya da tsada ake siyen dila. Da sai ki soma ko da da dila ɗaya ne kina turawa gida. Da zaran kinga harkar ta karɓeki sai ki dulmiya kuɗi a dama dake. Ga harkar zannuwan gado, ga harkar barguna ma itama tana tafiya( Anty Zee me zanin gado ana magana) ga atampa ƴar leda matan Najeriya na sonta sosai." Uwani dai ita damuwarta cikin dake jikinta ne, kuma a zahiri tana son taimakon iyayenta sosai. Kuma tasan mahaifiyarta ƴar kasuwace zata tsaya tsayin daka ta siyar da kaya in an tura mata yadda ya kamata. "To Hajiya kamar yadda kika ce sai in soma da dilar gumamar mu jarraba. Itama ƙawata bata buƙatar gidan aiki. Tana da kuɗi inma ba zasu isa ba, in nawa zai kai a sai mana dila biyu shikenan sai a siya mana. Mahaifiyata zata dinga siyar mana ana turo kuɗi muna tura wasu kayan." Hajiyarnan tace. "To da zafi _zafi ake dukan ƙarfe tunda dai da kuɗaɗenku dilolima akwaisu iri da kala a gidannan. Zan kaiku ku zaɓa sai ayi batun kuɗi. Sabida jirgin kayan ana ɗan samun jinkiri zaki ga bai isa da wuri ba. Kuma za a iya saro muku kaya daga can gida Najeriya kuma kuci kasuwarsu. Zaku fi ganin afkin kuɗin." Nan dai Uwani ta fito da kuɗi aka haɗa da nawa duk muka ɗungume kuɗi muka bata. Ashe wannan shine somin shigarmu cikin tarin tulin matsaloli. A taƙaice dai ashe damfara ce kawai Hajiya Babba ta haɗa domin ta karɓe wannan kuɗi da shi Abu Khadija da yaima Uwani ciki ya ambata mata ya ba ita Uwani. Gashi a gidan haya ake biya, kai zaka sai abinci da kuɗinka, kai zaka sai sabulun wanki da abun goge baki." Uwani dai tana kwance tana jinyar jikinta dan ta sha ciwon cikin da harna fidda rai da ci gaban rayuwarta. Cikin hikimar Allah kuma sai ya tashi kafaɗunta a cikin kwana na goma da zuwanmu gidan. Abinci bashi nake karɓa mana a wajen masu abincin gidan. Ƴan cirani babu irin waɗanda babu a gidan. Har mabarata mata da ƙananan yara akwai. A kwana na goma sha biyu sai gani a titi ina faɗin sabil_sabil ina kuka. Hajiya Zuwaira macece maras mutunci da rashin tausayi a hakan tazo take tambayarmu kuɗin hayar ɗaki wai kwana goma_goma ake biya. Watsi tayi mana da ƴar jakar kayan namu. Sai Fati wata yarinyace ta taimaka mana muka dawo ɗakinta. "Sai fa haƙuri. Amman me zai hana ku nemi gidan aiki. Tunda dai ba zaku iya irin rayuwar da mu muke yi ba, muma ƙaddara da wahalar aiki a gidan larabawa ne ya ja mana, kuma sai ka fi shekara nawa baka tara wani abun arziki ba. Ai ina ganin zai fi muku ko?" Ina sharar hawaye nace. Na amince zan tafi gidan aikin Fati. In shekara ta zagayo sai mu koma ƙasarmu abinda muka tara Allah ya amfana." Nan muka amince Hajiya Zuwaira ta sama mana gidan aiki. A can wani gari me nisa. Ni na soma tafiya wannan karon. Gidan wasu tsofaffin miji da mata aka kaini. Gidan akwai tarin aiki, ga tsofaffinnan da tsari, gasu da yawan yin baƙi. Haka na kama aiki ka'in da na'in kullum mafarkina bai wuce in buɗe idanuna in ganni a gida Najeriya ba. Ga dakon soyayyar Yaya Hamma da zuchiyata take ta faman ɗawainiya dashi. Duk tarin gajiya da tarin matsaloli daidai da sakan zuchiyata bata taɓa barin tunanin Yaya Hamma ba. ( Ina kira ga mata masu tsallake ƙasarsu su tafi wata ƙasar da zummar yin aiki. Ku sani in kinga wata taje ta samu kuɗi baki san irin sana'ar da take yi ba harta samu wannan kuɗin ba. Wasu har rasa rayukansu suke yi. Wallahi babu iriyar azabar da ba'a ganawa waɗannan mata masu barin ƙasarsu zuwa wata ƙasar. In baizo kanki bane kawai zaki ga kamar duk waɗannan abubbuwan basa faruwa. Amman akwai da yawa waɗanda suka shiga tarin matsalolin daya dama na su Iyabo ya shanye. Amman fa bance ba'a dacewa ba. Wasu suna iya zuwa saudiyya su ƙaraci rayuwarsu a gidan aiki ɗaya ba tare da sun sake ba. Kuma in har za a rabu ma kiga iyayen gidan sunyi ma ƴar aiki kyautuka na alfarma. Ƙalilanne masu dacewa da hakan. Da yawan yaranmu in suka tafi lalacewa suke yi su shiga harkar banza. Ke uwa, ko miji kuna gida gaho damuwarku ayi muku gini, a dinga turo muku kuɗi. Baku damu da halin da yaranku suke ciki ba. Kuma da yawan agait agait ɗinnan da yawansu basu da kirki cuta da ha'inci kawai suka saka a gaba. Da kin taɓasu sai suce suma hakan akayi musu. Ƙalilanne daga cikinsu zuchiyarsu take a tsabtace.) Gaga_gaga haka rayuwar tayi ta faman tafiya. Aiki kamar zai kasheni. Ba hutu, ga ciwon baya mai tsananin gaske da nake fama dashi. Musamman wayewar garinnan ta yau. Nama kasa miƙewa sallar asuba ma sai a zaune nayi. Gashi uwar ɗakina yarinyarta dake aure a Madina suna gidannan ita da yaranta huɗu tazo duba mahaifiyarta. In miƙe tsaye fa na kasa. Wallahi Allah sai da rarrafe na samu na fito. Ina ganin Uwar ɗakina na fashe da kuka nake cakuɗa mata larabci ina kwatanta mata zanje gida bayana ba lafiya. Hankalinta ya tashi. Take ta taso ƴarta aka ɗaukeni zuwa gida. A lokacin watana biyu da zuwa gidan kenan. Da ƴan kuɗaɗena a lalita dasu nake kwana kuma dasu nake tashi. Fati ce ta samu tawul da ruwa ta dinga dannamun bayan nawa, wanda a wannan lokacin har kumburi yayi. Ta mulke mun bayan da man zafi. Sai sannu wani ɗan daudu yake yi mun ƙawar Fatyne. "Subhanallaah ni kam ku rufa mun asiri kar ki mutu muna ɗakinnan ki jaza muna jafa i" Haƙorana suna kakkarwa nace dashi. Dama mutuwar zata zo ta ɗaukeni kaga shikenan nima na huta." Sai yayi shiru, can kuma yace . "Kinma ci abinci kuwa" Kai na girgiza mishi halamar A'a. "Kawo kuɗi a haɗo miki tea ki ɗumama cikinki, sai a ɗan haɗo miki da farfesu" Gudun kar susan akwai kuɗi a jikina, domin na fahimci rayuwar Saudiyya ba wanda yake yarda da kowa sai nace. Faty Ki ranta mun, dana samu dama_dama zan baki kuɗinki dan Allah" Cikin minti talatin sai gata da shayi me kauri da farfesun kaza, naci sa a na samu naman ƙirji. A daddafe na sha farfesun, na haɗa da tea. Magungunan ciwon jiki ta ɓaɓɓallo mun na watsasu. Cikin ikon Allah sai bacci ya ɗaukeni. Bani na farka ba sai da duhu ya rufa, dana miƙe tsaye sai naji da dama inji mutan nijar suka ce da dama. Alwala na ɗauro a ƙaramin toilet dake cikin ɗakin. Raak'a ɗaya na iyayi a tsaye, dana yi ruku'u kasa ɗagowa nayi sai zarcewa sujuda nayi, sabida ji nake dana tankwara bayan wani ƙashin ka iya ɓallewa in shiga uku. GWADABE MARAƊI Da daddare sosai Gwadabe ya shiga gida. Dan Hadiza ma ta ƙaraci jiranshi, da sunturin zuwa ɓarayinsu harta haƙura ta kwanta. "Kaine da daddare haka Gwadabe, ai daka raba tafiyar biyu." Cewar Auwala dake karɓama Gwadabe jakarshi. Sai da ya zauna daɓas a ƙasa yace. "Kai dai bari. Allah ya iso damu lafiya. Da fatan na sameku lafiya?" A tare suka waiwaya inda Mammada ke bacci yanata gwarti. Dariya suka saki su biyun. "Wannan matarshi ta shiga uku da wannan gwarti nashi" Cewar Auwala yana dariya. Gwadabe yace. "Kai kuma taka matar ta shiga uku da shegen cin abinci ba" Harararshi Auwala yayi. "Au to taka matar dame ta shiga uku, ko kai goma kake ba tara ba?" Dariya ya saka yace. "Ga gajarta ga tumbi" Dariya suka saka. Gwadabe dai ya miƙe ya samu ya watsa ruwa yazo ya rama sallolinshi. "Ga abinci Hadiza ta ajjiye maka. Tazo shashennan yayi sau talatin, gorin matan malam ne yasa ta haƙura, sai ta kawo abincin na ajjiye maka. Ammanfa tare zamu ci ato" Kai Gwadabe ya girgiza kawai. Ya jawo tiran silvern da kwanakin silven ke kai. Kwano na farko dafa dukan shinkafar manja ce da bushasshen kifi. Ɗayan ƙaramin kwanon kuma farfesun kazar Hausa ne, sai zoɓo cikin kofi me murfi na silver. Tunda ya buɗe abincin yaji yana wani irin ƙamshin spices na musamman. Da ya saka a bakinshi ji yayi tunda yake bai taɓa cin abinci mai daɗi da ƙamshin wannan ba. Yaci abincinnan da yawa, ragowar Auwala ya janye kwanon dan dole. "Auwala Hadiza ce tayi wannan girkin amman?" Saida ya yagi naman kaza kana yace. "Itace. Hadiza ba baya ba wajen iya dahuwa, damma bakaci miyar tuwonta ba. Lokacin da take gidan tsohon mijinta ina yawan kai mata ziyara kasanni da son sanwa" Kai Gwadabe ya gyaɗa yace. "Amman mijinta ya tabka babbar asara daya saketa." "Inji wa? Ko kai Hadiza tayi ma irin abinda tayi a gidan mijinta sakine zai tabbata a garete. Kai bata da daɗi fa wajen kishi. Kishinta na hauka ne. Kai dai kabi a hankali. Kuma Allah ne ya jarabceta shi yasa ma ta faɗo hannunka a lokacin da kai kuma tuni ka amshi soyayyar wata. Wallahi ba ƙaramin so Hadiza take yi maka ba da har ta amince da kishiya tun kafin aure ma" Gwadabe yayi shiru yana jinjina lamarin, tare da auna maganganun Auwala a ma'aunin hankali. Tsoronshi Allah tsoronshi tashin hankalin da zaije ya taɓa zumuncinsu. Kuma gashi ya kasance namiji mai son walwala da dauwakammen farin ciki a gidanshi. Amman yaci alwashin yin bakin ƙoƙarinshi na ganin bai kunna kishin Hadiza ba a cikin zamantakwar tasu. Yanata tunanin irin zaman da zaiyi dasu su biyun. Da waɗannan tunanin gari ya waye haske ya maye gurbin duhu. Nan samarin gidan suka soma layin yin wanka domin fita nema. Masu goge baki nayi, masu goge takalmi nayi. Gwadabe yana zaune a dakali yana jiran fitowar su Auwala. Sai ga Hadiza ta ratso hannunta rike da babban tire. Ƙurama takunta kallo Gwadabe yayi. A tsanake take yin komanta babu bankaure balle hayaniya. Saida ta kusan zuwa inda yake sai ya miƙe ya karɓeta Sadiƙu ya ja tsaki yace. "Aikin banza harara a duhu" Da Hadiza da Gwadabe duk suka waigo suka dubi Sadiƙu dake shirin ficewa a shashen. "Allah ya shirya. Barka da isowa Dijena" Murmushi tayi kawai ta dubeshi tace. "Ya hanya, ya ka baro kowa da kowa?" Fitowar Auwala ce ta katse amsar da Gwadabe yaso yaba Hadiza. Tiran kayan karin ya karɓe. "Ina kwana Yaya?" Hadiza ta faɗa tana haɗiye dariyarta. "Hadiza lafiya. Gwadabe zo da hanzari mu karya mu fice aikine damu sosai" "To Dijena kije, in muka dawo saimu samu mu tattauna, in kuma baki tsarabarki. Amman naji daɗin yin tozali dake, kuma na yaba da abincin da kika girka mun" Farin ciki fal zuchiyar Hadiza tace. "To godiya nake yi. Nima yanzu wajen aiki zan tafi, in ka dawo ma tattauna ƙila bakasan ina fita aiki ba. Sai kun dawo Allah ya tsare" Juyawa tayi ta kama hanya. Gwadabe kuma ya shiga ciki, suka gama karyawa tsab, aka fita nema. Basu suka dawo ba sai bayan isha yau sunyi dare. Suna dawowa Mammada yayi wanka ya tafi zance. Auwala kuma ya shiga cikin gida ya karɓo musu abincinsu. Bayan sun gama ci, Gwadabe yayi wanka sai ya tura yaro yai mishi kiran Hadiza. Bata fi minti goma ba sai gata. Yana hangota ya miƙe tsaye. "Yau dai muje waje mu ɗan zazzaga muna tafe muna zanca Uwar gida sarautar mata" Gwadabe shi ya soma fita Hadiza tabi bayanshi, sai da suka fita waje ne suka jera. "Soma bani labari. Da safe kince zaki tafi aiki. Dama kina zuwa aikine bansani ba?" Murmushi tayi "Na fahimci abun ya tsaya maka. Dan in ba haka ba ba hirar daya kamata mu soma ba kenan. Amman tunda ita ka zaɓa Shikenan zaka ji. Dama tun ina gidan tsohon mijina ni madam ce ( malamar makaranta) Ina koyar da yara ƴan primary school, fannin arabiya, nike ɗaukarsu Qur'ani da wasu littattafai biyu. to bayan aurena ya mutu ne, sai malam yaje da kanshi ya nemi alfarmar a bani hutu in kammala iddata. To ranar monday na ci gaba da koyarwa. Kaji abinda kake son ji" Kai ya jinjina yace. "Ashe tare da Madam nake ban sani ba? Kinga in mu kai Aure zaki dinga koyar dani karatu in sha Allah. Yayi kyau ni bazan hanaki aikinki ba, dan Shafa ma tana aiki a Najeriya, kuma wanta ya roƙeni akan in akayi auren zata nemi aiki anan inta samu to." Lokaci ɗaya annurin dake kan fuskar Hadiza ya gushe. Shiru ya biyo baya, sai tafiya suke yi a hankali. Hardai shi Gwadabe ya kawar da shirun ta hanyar jefo mata tambaya" "Yaushe su Malam zasu dawo ne?" A taƙaice ta bashi amsar. "Babu wanda yasan ranar dawowar tasu" Shiru ya ƙara biyo baya, wani ɗan dakali Gwadabe ya gani sai ya dubi Hadiza yace. "Zauna ki huta sarauniyar mata, takawarki Lafiya. Kinsan bana son ki wahala" Dole dai sai da ya dawo mata da farin cikinta, ta hanyar furta mata kalamai. Zama tayi tana dariya. "To Hadiza nima inaso zuwa gobe in soma sana'ar dafa magunguna na gargajiya. Wanda ya shafi na basir, maganin rana, da shawara, zan dinga ajjiyewa a wajen aikinmu. Sai ki taya ni da adda'a, in Allah ya taimakemu sai kika sana'ar ta karɓeni" Sun jima suna taɓa hira, daga bisani kuma suka koma gida, shi yayi shashensu, itama tayi nasu shashen. Kwana Gwadabe huɗu da dawowa, Baba Fhatsima suka dawo suma da daddare. A washe gari Malam ya tattare kan iyalinshi harda na gidan auren. Bayan Baba Fhatsima ta rarrabawa kowa tsabarshi, Malam ya soma magana. "Maƙasudin wannan taron dai shine zaman lafiya da haɗin kai. Ni da kaina na roƙeku da ku daure ku haɗe kawunanku, ko dan haɗin kan ƴaƴanku. A ko da yaushe a cikin fargaba da damuwar rashin haɗin kan iyalaina nake kwana in tashi, lamarin da ya kusan haifarmun da ciwon zicciya. To a wannan karon duk macen data nuna taurin kai, ko ta hana yaran ɗakinta yin biyayya a kan dokikina to magana domin Allah zan sallameta. A yanzu in ganku kayukanku a haɗe shine babban abinda ke gabana." Take aka shiga ƙusƙus a falon. Malam yayi shiru yana kallonsu kafin ya ci gaba da cewa. "Doka ta farko shine, dole ko wanne yaro a cikin gidannan da safe yabi ɗakunan matana kab ya gaishesu wajibine wannan, duk wanda ya saɓa zai gamu da abinda baiyi zato ba balle tsammani. Kuma tun yanzu inaso yarana in cakuɗesu a ɗaki ba kamar yanzu da suke a wawware ba. Ina nufin Mammada zai koma Ɗakin su Sadiƙu, shi Sadiƙu ya koma gadon Mammada, Sabitu kuma ya koma cikin su Zailani, shi zailani ya koma ɗakin su Safiyanu. Haka dai nakeso ya canja, domin su soma sabawa da juna tun kafin su yi aure. Sannan a yarana kab, da matan nawa duk me son wani abu daga gareni ga Tasi'u na ɗaura mishi duk nauyin. Wanda yasa girman kai sai ya haƙura. Shine magajina, Babban wa uba, dole a bashi matsayinshi" Baba asshi ce ta miƙe tare da cewa. "Malam inada..." "Dakata Asshi. Wannan ba malam ɗin da kika sani a shekara talatin baya bane. Ki zauna ban ba kowa izinin magana ba, asalima bana buƙatar maganar kowa. Duk matar da taji ba zata iya bin dokikin gidana ba, ƙofata a buɗe take" Jin irin yadda Malam yake faɗa sai kowa ya shiga taitayinshi. Malam ya dinga tsaro yanda yakeso ayi. Abinda ya kamata ace tun sanda yara suna ƙanana ya kamata ayi, shi malam sai yanzu akeyi. Kuma wannan ya farune a bisa yanda Malam ya kasa zama tsayayye a gidanshi. Ya sake ko wacce mace inta shiga da irin abinda take shigowa dashi. Shi kuma ya kasa taka burki a gidan nashi. A haka gidan ya cika da yara, a lokacin da yaran suke ƙanƙana babu irin rikicin da ba'ayi a gidan. Uwargidan Malam ce kaɗai mace mai haƙuri da kawaici. Itake ke iya kawar da kanta in matan malam nayi ma yaranta hukunci, kuma mafi akasarin hukuncin na son zuchiyane. Babu irin hawala da makircin da Baba Fhatsima bata gani ba a wajen Baba Asshi ba. Dan har takai ta kawo malam ko ƙofar ɗakinta baya iya kallo in ba ranar kwananta bane. Ta baza mulki tayi abinda takeso. Sai da malam ya sake auro mace ne Baba Fhatsima ta samu sassauci a gidan, domin kishi an kasafta gida biyu a lokacin. Malam kuma duk matar daya auro saita kasance itace ta gaban goshi a wajenshi, harma baya iya ɓoyewa, hatta cefanan ranar girkinta dabanne kawai. Ire_iren waɗannan halayyar ta maza ta rushe haɗin kai da zaman lafiyar haula da dama. MRS BUKHARI *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* Domin neman ƙarin bayani 07082649563 whats app number kira 07036028230 [8/15, 8:43 PM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BOOK 2 BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 10 Haka sabuwar rayuwar gidan Malam taci gaba da kasancewa. Yaran basu da wani zaɓi face su bi umarnin mahaifinsu. Yayin da daga bayan fage iyayensu mata ke musu huɗubar tsiya, tare da cusa musu tsanar Baba Fhatsima da yaran ɗakinta. Ko gaishe da Baba Fhatsima suka je yi, cikin wulaƙanci da rashin girma suke gaisheta. Itako Baba asshi ko kallon inda Baba Fhatsima take bata yi, ƴar gaisuwarma sun dena, domin tunaninta shine Baba Fhatsima ta murɗa kambunta ta sake ƙwace gida a karo na biyu. Dan in ranar kwananta ne Malam ya dinga sunturi kenan a tsakar gidan. Itama in kwananta ne, zata shige turaka ta nitsu ta yi gyara na musamman a kunna turaren wuta. Da yamma taci adonta da kaya masu tsada tayi tafiyarta turaka. Wannan sauyi na Malam da Baba Fhatsima ya tsayama matan gidan daram a zuchiyarsu. Yayin da wasu suka soma sake sabon salon kula da malam, su Baba Asshi kuma bata da aiki sai ya da habaici a tsakar gida. Kuma taci alwashin ba zata taɓa tambayar Tasi'u kuɗi ko yai mata wani abun ba. Itama tana Ɗa Jamilu, kuma dai dai gwargwado shima yana samu, saidai Allah yayi shi da shegiyar rowa, dan ko matarshi Siyama da ƙyar take ɓamɓararshi. Tasi'u ya dage sai gini aketa faman yi, abunka da kuɗi gininnan bai jima ba aka kasheshi, har an soma buga rabta. Ta wani ɓangare harya gama siyen kayan gado, da kujerun ƙannenshi mata, sauran tarkacen kitchen iyayensu mata ne zasu yi musu. Ya kuma riga ya sallami Baba Fhatsima da ishasshen kuɗin kayan kitchen ɗin Hadiza, da kuɗaɗen gudanar da harkar sha'anin bikin al'ada. A ranar da yaba Baba Fhatsima kuɗinne tace. "Su matan Babanka ka basu kuɗin da zasu gabatar da sha'anin bikin al'adar ne, kasan fa ana kashe kuɗi musamman ga su da zasu aurar da maza. Kuma jibi ma za'aje kan goron mazan gidan. Jibi kuma Malam zai tafi Takai yaje ya sanar musu da lokacin biki" Tasi'u yace da Baba Fhatsima. "Baba ban ba ko wacce daga cikin su ko sisi ba. Sabida a tunanina tunda auren maza zasu yi su yaran zasu bama iyayen kuɗin komai. Yarannan ba ganinki suke da gashi ba" "Hatta Malam basa ganinshi da gashi. Kai dai kai musu domin Allah domin kuma uwayenka ne. Hatta Amaryar malam nasan zata yi nata taron, da anko duk zata yi naga sai fitarwa akeyi kashi_kashi. Itama ka bata abinda zata yi hidimarta dashi. Allah yayi albarka" Shiru yayi can ya girgiza kai yace. "Babu komai za'ayi musu kamar yadda kika ce, in sha Allah. Naga yaronnan Gwadabe yayi ƙoƙari wajen haɗa akwatunan bikin. Sune can ko? Badi'a ta faɗamun yasa kaya masu tsada ba laifi, ta yi goshi a matsayinta na Bazawara " Baba Fhatsima tayi dariya. "Yayi ƙoƙari babu shakka, Allah ya fiddamu kunya. Dan Allah ya buɗe musu kwanakin baya sosai. Kaga zinarin da suka tono yana da nauyi ainun. Shi ya taimaki harsu Auwala suka ƙarashe haɗa akwatunan nasu. Kuma sana'ar magani da yake yi matan gidannan na dariya suna tsokanar Hadiza wai taci baya. Sana'ar na taimaka mishi, ana siyen magungunan nashi sosai. Naga har almajiran malam siye suke yi. Kaga akwatin kishiyar Hadizan ma, komai iri ɗaya ya zuba har kala. Shine ma take ta ƙorafi ƙasanta da rashin hankali. Da abokinshi ma ya ɗauke mishi akwatin ita waccan ɗin, da dai ya samu halin yine yace zaiyi abinshi" Jawo mishi akwatunan tayi gabanshi, komai na ciki bai bambanta ba, girman takalmi, ɗan kamfai, rigar Mama shine kawai na ɗaya ya zarce na ɗaya. Dariya Yaya Tasi'u yayi. "Hadiza daru ba. To na ƙara mata ko kala biyar ne" Baba Fhatsima tayi dariya itama tace. "Rabu da'ita. Ta haɗa kaya famtimoti Babba, kuma duk ta ɗinka abinta. Ga malam yayi musu kayan fitar biki. Ai kasanta da kishi, kullum cikin faɗa nake mata. Jibi Babarku Altine tana hanya zata zo ita da Balaraba ƴar wajenta. Kuma inajin sai an gama bikinnan zasu koma." Altine ƙanwa take ga Baba Fhatsima. Mace mai kirki da son zumunci. Sai dai ba'a wanyewa lafiya tsakaninta da matan malam. Dan bata barin ko ta kwana. Balaraba kuma ɗiyarta ce, wacce da akaso ayi musu haɗin gida da Tasi'u. Amman a lokacin Tasi'u ya riga ya soma soyayya da matarshi Badi'a. Sai Balaraba ta auri saurayinta dama tana da saurayinta iyayene suka so ayi haɗin gida kawai. Yanzu kuma Allah yayi ma mijin nata rasuwa ya barta da yara bakwai. "Allah sarki. Mama altine jibi ana hanya? To a ɓarayina zasu sauka gaskiya wannan karon ƙwaceta zanyi." Haka dai akaita hidimar biki ta ko wanne ɓangare, gidan a kacame yake ko da yaushe. Washe Gari akaje kan goron Samarin gidan tare da kai fantimoti. An tsayar da biki wata biyu cib. Ranar a gidan ba'ai girki ba, abincinan da aka tawo dashi daga kan goro ya isa har maƙota sunci shi a wadace Washe gari Malam da Jamilu suka kama hanyar Takai a motar Jamilun, tare da akwatin Shafa wanda daga nan za'a kai nan gidansu Shafa dake Takai ɗin. TAKAI TA KAWO TA SABA DA SAUKAR BAƘI Babala tana zaune a tsakar gida, ta jiyo yaran gida na yima Baba Magaji sannu da zuwa. Sai taga akwatuna Bara'u na shigowa dasu. "Kai Bara'u waɗannan famtimotan fa shi Yaya Magaji shine ya tawo dasu?" Murmushi Bara'u yayi yace. "E dashi suka tawo. Kinganshi ma ya shigo" Yana kaiwa nan ya fice. Yaya Halima da Goggo Iyatu suka fito daga ɗaki riƙe da haɓa har Yaya Magaji da Jamilu suka ƙaraso. "Maraba lale da zuwa, Jamilu yau kaine a cikin gidannan iko sai Allah. Wasa gaske Gwadabe naso ya dawo da tsohon zumunci" Cewar Babala data haɗe ranta tayi kicin_kicin. "Baba ku shigo daga ciki, kunsha hanya, ga magriba tayi." Cewar Yaya Halima kenan. "A'a Uwata bamu ruwa a buta kinji magriba ake kira, in muka yo Sallah mazo a tattauna a tsanake. Hambali bai ƙaraso bane, na kirashi shi da Harisu nace duk mu haɗu anan." Goggo Iyatu tace. "Yanzu fitarsu masallaci kuka iso" Ruwa aka basu a buta su kai alwala tare da tafiya masallaci. Tare suka dawo dasu Yaya Hambali. Abinci aka dire musu. Baba Magaji da ya kai loma bakinshi bayan an gaggaisa sai ya soma jawabi. "Wannan fantimotin auren Gwadabe ne, da Shafa ƙanwar abokinshi Tamu, ƴaƴan mirgayi Hamisun Dogo. Da daddarennan nake son za'a kai kayan tare da sadaki baki ɗaya. Wannan dalilinne yasa nace Hambali da Harisu su tawo dan su jagoranci komai tunda sune manya." "Kaga ni Yaya ban gane me kake nufi ba. Au jita_jitar da muke ta ji a gari akan Shafa Gwadabe zai aura ashe da gaskene itan zai aura. Ina batun Hadiza ƴar Fhatsima?" "Du su biyun zai aura kuma rana ɗaya da izinin Allah " Dariya Yaya Hambali ya saka. "Ikon Allah waina kwance ya faɗi. In banda talaka da nemo wa kai jarfa ina Gwadabe ina mata har biyu Baba. A duba lamarinnan fa, kar a siyar da akuya ta dawo tana cin danga. Dan Gwadabe ba mai ƙashin ma arziki bane shi tun fil azal, duk abinda yaronnan ya taɓa sai ya lalace. Yanda Allah yaimun wannan sutura bana jin zan iya shiga wata hidimar Gwadabe, ko dan gudun kar jarfar dake bibiyarshi ta shafeni." Jim Baba Magaji yayi, yana kallon Yaya Hambali da maɗaukakin mamaki. Yaya Harisu yace. "Ni kaina bazan iya saka hannu a duk wata hidimar Gwadabe ba. Yaron dake tafiya da bakin uwa" Jamilu ya buɗe bakinshi dan mamaki. Goggo Iyatu kuwa sai sharar hawaye take yi. "Ohh Yaya Laila ce dai baka ƙaunar Gwadabe ya aura. Amman gashi ka jona mishi ƴarka kai. Yarinyata ta ƙi zaman aure, yanzu haka tana gida an sake sakota, bayan mijin yayi mata kafirin duka." "Hmmm ni kam nama rasa ta cewa wallahi. Yaya Gwadabe kaima ɗanka ne. Kai kaɗai gayyane zaka iya zartar da komai. Gidansu Shafa ka sani. Allah ya sanya alkairi shine kaɗai abinda zance. Amman Gwadabe ai ya nuna mun bai haifu a cikina ba. Tunda ni ina matsayin uwarshi sai dai in ji ƙishin_ƙishin a gari zai auri ƙanwar abokinshi. Yaranshi duk ya tattare ya damƙa mishi. Gashi da ƴan uwa ya nuna baya ƙaunarsu. Damme zasu ƙaunaceshi shim... "Ya isa haka nace" Baba Magaji ya dakatar da Babala da kakkausar murya. "Lallai Babala ba zaki taɓa yin hankaliba har abada. Ke da kanki kike farraƙa kan yaranki. Shin me Gwadabe yayi miki ne a rayuwa haka. Ba dai akan Auren beyerabiya bane? To naga ya rabu da'ita. Na ɗauka ƙiyayyar zata tsaya a iya nan ki sama yaronnan albarka ko zai ga haske. Me yasa kika zame mishi baƙar uwa? To Shikenan ni zan tsaya mishi ayi komai. Ku kuma" Ya nuna su Yaya Hambali yace. "Kubi duniya a hankali. Ita dukiya baƙuwace. Kuma wanda Allah yace sai yayi arziki sai yayi. Ina jiye muku ranar da zaku kasa haɗa idanu da Gwadabe, ko kuma ranar da zaku kasa matsowa inda yake sakamakon ɗaukakar da zai samu. Jamilu ci abinci ka kinkimar mun famtimotinnan muje kai da Bara'u ku rakani na ishi Gwadabe uwa da uba. Ƴan uwanshi na can sun share mai hawayenshi, suna sonshi, kuma suna zumuncinsu. Akwai ranar ƙin dillanci. Yaya Halima ta buɗe baki zatai magana, Baba Magaji ya dakatar da'ita ta hanyar ɗaga mata hannunshi. Matan gida suka shiga tururuwar zuwa gaishe da Baba Magaji, daurewa yayi ya dinga fara'a dan kawar musu da tunani. "Gida naga yasha gyara, waye yayi muku gyara haka" "Ka ganshi ɗan albarka wanda tun yana tsumman goyo yake samun tabarraki. Allah yayi mishi lifiɗi yayi gamdakatar da arzikinshi. Kuma ya ja ƴan uwan nashi a jiki anata harkar arziki. Nanda wata biyar ma umara zamu dani dashi da matar tashi." Babala ce take magana da fara'a sai dariya take yi. Baba Magaji yace. "Madallah Allah yaima dukiya albarka Hambali. Jamilu muje ko?" Tashi Jamilu yayi ya soma jan famtimotan zuwa waje. Yana jaye dasu Baba Magaji yana biye dashi a baya. A ƙofar gida suka tarar da Bara'u duk suka rankaya. Sun samu tarba ta mutunci gaya. Nan suka gabatar da sadaki da kayan aure. "To nan da wata biyu dai muke so a ayi komai a gama. A duba, sabida tare muke son ayi komai a gama yarane kusan goma za'ayi bikin nasu tare" Ƙannen mahaifinsu Shafa ɗaya daga ciki yace. "Allah ya nuna mana lokacin. Yaro yayi mana bayanin komai. Mu dama mun daɗe a shirye. Fatanmu Allah ya kai rayuwarmu" Nan su kai sallama da juna. Ta ɓangaren Babala daren ranar kasa bacci tayi, ta saƙa wancan ta kunce wancan. Babu irin abinda bata hasaso a ranta ba dangane da irin abinda Baba Magaji yayi mata. Abun ya matuƙar ɓata ranta har kuma taci alwashin ba zata taɓa taka ƙafarta da sunan zuwa bikin Gwadabe ba. Kuma ƙafarta ba zata taka dan matanshi sun haihu ba. Kuma taci alwashin duk ranar da ya tako ƙafarshi yazo inda take sai tayi mishi tijara. Da waɗannan ire iren tunanin garinta ya waye. Ta ɓangaren Baba Magaji ma, sai tunani yake yi, tare da jinjina halayya irin ta Babala Haka ta taso tun asali da wata iriyar baƙar zuchiya mai shegen riƙo da rashin yafiya. Uwa uba ga jahilci da zaman karkara dake ɗawainiya da rayuwarta, in banda haka taya uwa zata dinga adawa da gaba da duk ci gaban ɗan data tsugunna ta haifa, akan dalilin da ba dalili ba. Ko washe gari kafin Baba Magaji ya tafi sai da ya sille Babala tas, itama kuma ta fusata dashi, dama a wuya take dashi nan tayi tsalle ta dire tace. "Magaji dakata kaji, ba zaka zo har gidan mijina ka nemi tozartani a gaban ƴaƴana ba. Sabida haka kar ka sake tako ƙafarka kazo inda nake, ka soma gyara gidanka tukunna, ka dena rashin adalci a tsakankanin matanka tukunna kafin kazo mun da guntun wa'azinka. In aka sake faɗamun wani abu daya danganci Gwadabe ma Allah ya'isa ban yafe ba. Ka faɗa mishi matsawar ya tako Takai da zummar zuwa ganina nonona da yasha sai ya biyani. Haka in ya tako ƙafarshi yaje wajen ƴan uwanshi Allah ya isa ban yafe mishi ba ehe, kaje ka riƙeshi" Idanu Baba Magaji ya runtse. Yaya Hambali kuwa ya saki wata siririn murmushi, Yaya Harisu kuwa fuskarshi kadaran kadaham. Matan ƙannen mijin Babala nan suka shiga bata haƙuri tare da nuna mata rashin kyautawarta akan furucinta, gudun kar ta sake ɓalɓanta rayuwar Gwadabe da ci gabanshi. Amman suma sai ta dira a kansu. Baba Magaji yace. "Ki rubuta ki ajjiye, daga Gwadabe har ni ba zaki sake saka kowa a idanunki ba. Jahilar kawai tur dake a matsayin uwa ga Gwadabe. Ki sani wata rana zaki shiga jerin masu layin son yin tozali da Gwadabe." Yana kaiwa nan ya ja hannun Jamilu rai a ɓace yana share hawayenshi. Itama ta shige ɗaki fuu su Yaya Hambali suka mara mata baya. "Wallahi ina shirin taka mishi birki kenan kika tanka Babala. Akan mitsiyaci Gwadabe za a shigo har fadarki ai miki ɗiban albarka. Anya Baba Magaji yana ƙaunarku kuwa?" Cewar Yaya Hambali " "Inafa yake ƙaunata. Ai Shikenan babu kare bin damo, yaje gashi ga Gwadaben, shima bai iya gyara gidanshi ba, ya kasa haɗe kan matanshi sai gidan wasu zai shigo ya gyara" Baba Magaji" Yana zaune a bayan mota, sai tunanin irin furucin Babala na rashin albarka yake yi. Abu biyu sune suka tsaya mishi. Na farko cire Gwadabe daga cikin ahalinta. Na biyu kiranshi da tayi ba adaliba wannan ya taɓashi, hakan yasa ya sake ɗambar ganin kan gidanshi ya haɗu, duk da shi kanshi ya sani abune mai kamar wuya" Basu suka isa Maraɗi ba sai wajajen goman dare. Da sallama suka shiga gidan, matan gidan sai hada hadarsu suke yi a tsakar gidan, ko wacce kaji muryarta ta to da yaranta take hirarta. Sannu da zuwa suka yi mishi, rannan nashi a mugun murtuke ya wuce ɓarayinshi. Yana wanka Baba Fhatsima ta shigo, yana jin shige da ficenta, ɗaure da babban tawul ya fito. Idanu ya zuba mata tayi kwalliyarta sai wani dattijuwar kyau take yi. Ajjiyar zuchiya ya sauke, Fhatsima tana daga cikin matan da kallonsu ke kawar da damuwa, gami da mantar da ɗa namiji inda ya dosa. "Maraba da dawowa ranka shi daɗe babban malamina" Zama yayi a kusa da'ita. "Barka Fhatsima da fatan na sameku lafiya? Na yi ma Allah godiya daya kasance lura dani a cikin wannan daren yana hannunki, ƙila da sai dai a wayo gari zuchiyata ta buga. Dan kece kaɗai mai iya mallakata" Farin ciki ne ya lulluɓe illahirin jikin Baba Fhatsima. Abinci ta zuba mishi suka dawo falo. Yana ci tana mishi taɗi ananne ta sanar dashi zuwan Altine ƙaunarta da da Balaraba "Allah sarki Altine uwar zumunci yanzu harta zo dan ayi komai tare da'ita. Yaya mijin nata da surukanta?" "Suna lafiya dukkansu. Ina ruwan Altine daru, ko ɗazu sai da su kai ƴar hayaniya da sahibarka Asshi" Murmushi yayo yana ƙoƙarin karantar yanayinta. Kishinta na mallakar kai yana burgeshi, tana da tsantsar kishi, amman kishin da bai rufe mata idanun da zata cuta ma abokan zamanta ba daidai da kalma. Kishin da bai gusar mata da nutsuwa da kamalarta ba. Yanzu ambaton ashshi kawai da tayi, sai da hancinta ya ɗanyi wani doro, wanda da wannan doron hancin Malam ke gane tana yanayi na kishi. Ɗauke tunanin nata yayi ta hanyar cewa. "Hmm kinsan yanda muka kwashe da shashashar yarinyarnan kuwa?" A nutse ta kalleshi tace" "Da naso ne ka nutsu tukunna ko zuwa da safe saimu tattauna, domin sake maimaita maganar a cikin yanayin fishi ka iya haifar da wani fushin." Da wannan Baba Fhatsima ta rinjayi mijinta. Ta ɓangaren angwaye kuma sun sake zage damtsen neman na tuwo, biki sai ƙaratowa yake yi gida yayi kace kace. Gwadabe bai san halin da ake ciki ba, domin Baba Fhatsima ta ba Malam shawarar ya rufe zancan har sai zuwa bayan biki sai yai mishi bayani a tsanake. Gidan Amare yayi shar dashi ya ɗauki fenti gabaki ɗaya harda cikin gidan malam. Yara kuma sun gwangwaje iyayensu da gyaran daƙuna suma dai sun zama amare a wajen Malam. Malam da kanshi ya tusa angwayennan gaba ko wanne ya zaɓi ɗakinshi duk zubinsu iri ɗayaa ne babu wani bambanci, Gwadabe dakunan matanshi suna jere, a kusa da ɗakin Sadiƙu, kafin ɗakin Gwadabe kuma ɗakin Auwala ne. Key Malam ya miƙama ko wanne. Su Tasi'u da Jamilu su zubin ɗakunansu yafi yalwa, kuma ɗakuna uku ne a ciki kasancewar suna da yara maza da mata. Malam ya basu umarnin ana biki saura sati guda su dawo wannan ɓarayin amare su shigo su samesu a ciki. Haka dai akaita shidimar biki. Ana saura sati guda ɗaurin aure baƙin nesa suka soma cika gida. Su Anty Badi'a kuma suka ƙaura izuwa sabon gida. Nan malam kuma yasa aka fente dakunan da suka tashi wanda Tasi'u ya fita yace Baba Fhatsima ta koma ciki. Wanda jamilu ya fita kuma yaba Baba Asshi. Nan Suwaiba da Amaryar malam suka shiga tashin hankali da tunane tunane dan su a tunaninsu tunda dai su da sauran mammora a jikinsu su ya dace ace Malam yaba waɗannan ɗakuna ba matanshi tsofaffi ba. Ta bangaren Amaren gidan malam su su huɗu sai gyaran jiki aketa faman yi musu. Magunguna kuwa a dama musu wannan da madara, wannan a dama da Nono haka dai aketa faman yi musu. Hadiza dai tunda baƙi suka cika gidan nasu bata saka gogan nata a idanunta ba, wayarma ba kasafai suka fiye yinta ba. Ita dai sai tsuma kanta take yi, burinta ta zama sarauniyar zuchiyar Gwadabe. Kuma kasancewarta bazawara harda yara yasa tafi ƴan matan kannenta shirya kanta. Ƙawarta Hassana itace take ta bata dabaru da sirrin zama da kishiya, sakamakon ita a gidanta itace ta uku. Hadiza ta ɗaura ɗamarar yaƙi da jahilin kishi, ta ɗaura ɗamarar bama Gwadabe farin ciki, da kiyaye dukkannin ɓacin ranshi. Amaryarshi kuma tsakaninsu gaisuwane, dan bata jin zata wani iya zaman hira ko wani sakin fuska da kishiya. Kowacce dai ta iya allon ta ta wanke. Kasancewarta Amaryar ƴar gida har an mata jerenta tsab, ta samu kaya fiye da aurenta na fari, ɗakinta yayi matuƙar kyau. Tun kafin gida ya cika da mutane Baba Fhatsima da Goggo Altine su ka zaunar da Hafiza sukaita karanta mata karatu masu amfani ( gaba cikin labarin zamu ji me suka faɗa mata a aikace a gidan Gwadabe) Duk abinda suka faɗa mata tayi ram dasu a ƙwaƙwalwarta sai jujjuyasu take tana farin ciki. Harma Allah _Allah take a soma wasan. Rana bata ƙarya Allah ya kawo mu ranar biki. Tun ranar Monday aka soma shagulgulan da suka shafi al'adu, ta ɓangare Amare da angwaye. Ta bangaren ƴan Takai. Goggo Iyatu, da Goggo Rahila Matar ƙanin Babansu Gwadabe ne a manya suka tawo. A yaran mata Laila tazo, sai Abuwa matar Ɗan Goggo Hajiyayye matar Ƙanin mahaifin su gwadabe, ita tsufa ya kamata Abuwa ke wakiltarta zuwa duk wani sha'ani na dole. Babala dai dasu Yaya Hambali da matansu ko ƙeyarsu babu. Gida ya kacame da sha'ani. Mayu da ɓarayi sun samu abun nema, kowa sai farauta Laila kuwa duk abinda taga anyi wasarere dashi saita adanashi, ta sake ta shiga jami'a sosai. Duk wanda yai wasarere da jakarshi, akwai Laila da ire_irenta da yawa a gidan biki su zasu adanama mutum kayanshi hausawa sukace mai son abinka ya fika dabara. Amare sai kyau suke sha, su saka wannan sutura su canja. Hadiza tayi kyau fiye da aurenta na fari, domin yanzu tafi sanin kanta fiye da baya, a baya akwai ƙuruciya. Amman a yanzu tasan cikakkiyar darajarta ta ɗiya mace. GWADABE: Ranar da aka ɗaura aurensu Hadiza da safe, Gwadabe nata shirin kama hanyar Najeriya shi da Baba Magaji. Sai ga Auwala ya shigo ɗaki ya sameshi sun sha uban ankon farar shadda mai maiƙo. "Ango mijin Hadiza. Malam ne yace in yi kiranka zaku yi magana" Murmushi yayi mishi yace. "Ango mijin Zakiya bada kan ka a sare kaje gida kace ya faɗi" Dariya suka saka dukkansu. Hularshi ya ɗakko yasa suka fita tare. Ratsa mata ƴan biki sukayi, sai nunasu akeyi gwanin sha'awa duk kaya iri guda suka saka harda su Yaya Tasi'u. A zaure suka samu Malam da aminanshi dattijai biyu. "Gwadabe tafiyarmu Najeriya an fasa. Yanzu haka maganar da nake maka an ɗaura auren naka acan Tamu da Bara'u su suka tsaya akan komai, yanzu aka ɗaura auren. Sun kirani suna hanyar tawowa da Amarya, motar kaya kuma tun jiya da rana ta kamo hanya. Babu mamaki zuwa rana ka gansu. Na sanar ma Fhatsima Dangin amarya da masu jere suna hanya. To sai ka zauna a cikin shirin tarbar amaryarka" Murmushi Gwadabe yayi, kanshi na ƙasa sai godiya yake yi ma Malam kawai, domin bashi da bakin gode mishi, yayi mishi komai a rayuwa. Sallamarsu Malam yayi suka fice waje wajen abokansu. Hadiza: Ta bangaren Hadiza tunda Malam ya sanar ma Baba Fhatsima Amaryar Gwadabe suna hanya. Sai cikinta ya ɗuri ruwa, har wani zazzaɓi taji yana shirin sakko mata. Goggo Altine ta dubi Baba Fhatsima tace. "Zuwa bayan la'asar sai a shigar da ita gidanta tunda itace uwar gida, yana da kyau Amarya tazo ta sameta a ɗakinta. Dan haka bari in fita in sanarma da su Hadizan Zendar." Wani sanyi Hadiza taji ya kwaranyi daga kanta zuwa ƙirjinta. Kafin azahar masu jere suka iso motar jere daban, motar iyaye daban. Sun samu tarba ta arziki an taresu da kaji da farfesu, da tuwon ɓula ( tuwon ruwa) Ana idar da sallar La'asar aka fito da Amarya Hadiza. A zaure suka yi kaciɓus da Malam yana tsaye yana jiran fitowar tasu. Tsugunnawa Hadiza tayi tana hawaye a gaban Malam. "To Hadiza ina fatan wannan fitar da zaki yi daga gidanku yasa fitace ta har abada sai dai zuwan daɗi in sha Allah MRS BUKHARI Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 [8/21, 8:11 PM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 11 Ga wannan a rage zafi zuwa monday zan dawo ka'in da na'in 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. "Na horeki da haƙuri da kawaici. Kiyi zaman aure irin wanda mahaifiyarki take yi. Sannan kiyi kishi irin nata Hadiza. Allah yayi albarka Allah yasa sai dai a fitar da gawarki. Ga wannan ɗan kunnen zinarin ki adanashi zai miki Amfani, ko da zaki siyar ki tabbatar juya kuɗin zaki yi ba wasa dasu ba. Altine ku tafi da'ita" Altine ta ɗaga Hadiza suka fita aka kaita ɗakinta. Barinta akayi ita da ƙawayenta sunata hirarsu. Ƴan uwan Shafa kuma sai jere suke yi mata dan a gaskiya Shafa tafi Hadiza kaya musamman kayan ƙawa na ɗaki, dangin samiru da kwalla. Kuma sai da aka mata bango guda na kwalliyar tasa, sai ɗaukar idanu suke yi. Duk labari ya isarma Hadiza, sai taji babu daɗi domin ba hakan taso ba. Ƴan kuɗaɗen data samu na gudunmawa ta ɗungume ta ba Aminiyarta suka ƙaro mata kumbula da kwalla. Kafin magriba har sun dawo, suka kuma sherawa, tare da sake ma ɗakin fasalin daya dace. Ta bangaren angwaye ana fitowa sallar magriba ko wanne ya jaye abokanshi suka nufi cikin gida domin gabatar da WATSI. Inda ake ma ango watsin alawa, da kuɗi. Ana samun kuɗaɗe sosai. Ko wanne ango dangin mahaifiyarshi ne suka shimfiɗa musu taburmai. Akaita watsin kuɗi da cingam. A wannan rana angwayen sun samu kuɗi na mamaki domin wannan ranar tana daga cikin ranakun nuna bajintar dangi, da amfanin tarin dangi. Su Gwadabe sun samu kuɗi sosai a wannan rana dan dangin Baba Fhatsima masu kuɗi rabinsu da kwata suke Aure, uwa uba ga Yaya Tasi'u shima ya nuna bajintarshi, da yarsu Zarah. Wankan kudi kawai akaita musu, lokaci ɗaya kallo ya dawo wajensu Gwadabe. Mata sai ihu da guɗa suke yi. Dangin Baba Fhatsima sukaita musu ɓarin kuɗi kawai. Kiran sallar isha ne ya dakatar da abun. Nan suka kwashe kuɗaɗensu a buhu suka yi gaba. Nan kuma aka shiga kawo amare ɗakunansu, tare da bataliyar ƙawayen Amare. Da misalin sha ɗayan dare gungun motocin ƴan kawo Amarya suka iso ayari guda. Bus biyu, da karamar mota biyu, ƙaramar mota ɗaya ta amarya da ƙawayenta ce, ɗayar ƙaramar motar ta abokan Gwadabe ce, Bus ɗinnan kuma yaran mata da tsofaffi, da yara ƙananu ne aka kwasosu, kunsan dai yanda ƴan ƙauye suke tafiya raɓaɓe _raɓaɓe da bataliyar yara. Cikin gida aka shiga da iyaye tsofaffi, da yaran mata. Ƙawayen Amarya da amarya kuma aka barsu a ɗakin amaya. Su Bara'u kuma suna waje sun haɗe cikin samarin maraɗi sai shan gahawa da gashasshen nama suke yi. Kofar gidan malam kamar rana tsabaragen taron maza abokan angwaye, kowa ya haɗa dabarshi da abokanshi. Ga almajiran malam sai daudalar cin tuwo suke yi anata nishaɗi. Cikin gidanma haya_haya duk inda ka kutsa. Duk an zube a tsakar gida sabida yanayi na zafi ga tarin jama'a. Ƴan Takai sun samu tarba da abinci lafiyayye da soyayyun ƴaƴan shila harda lemun limca, da 7up. Ƙawayen Amarya nama da shayi aka tarbesu dashi, sai bireɗensu suke yi. A tsakankanin Amare Takwas da suka tare a ɗakunan mazajensu. Ko wacce an zuba mata kaya wannan na wane wannan, ga gara ta ban mamaki da akayo musu, ko wacce ɗan ƙaramin kitchen ɗinta cike da kayan masarufi, wasu harda miyoyin kaji aka haɗosu, wasu kuma dambun nama. Ko wacce Amarya tana a tsakankanin ƙawayenta sunata farin ciki. Saɓanin Hadiza da Shafa da zuchiyarsu take cike da zulumi gami da fargabar haɗuwa da juna. Ko wacce a zuchiyarta tana fatan tafi ƴar uwarta ko da da abu ɗaya ne ta fannin halitta. Hadiza tafi Shafa shiga cikin damuwa dan ita hakan ya taɓa mata annurinta, sai tayi laƙwam ta yi tagumi tana kallon ƙawayenta zaurawa da matan auren da suka nace sai sun tayata kwanan ɗakin miji. Su kuwa sai dariya da bada labarin kishiyoyi, da irin makirce_makircen wasu matan suke yi. Ta bangaren Shafa kuma ita tsoronta ɗaya ne kawai, yanda take ji da ganin budewar idanun zaurawa da ilimin zaman aure da suka fi ƴan mata dashi, shine tsoronta, dan ta fahimci tamkar Gwadabe yafi bata lokacinshi fiye da ita. Amman da tamai ƙotafi sai ya nunar mata ba hakan bane yanayin aikine kawai ke hanashi kiranta a waya. Da Waɗannan tunane_ tunane dare ya tsala. Maza a ƙozar gida suka kwana. Ƙawayen Amarya da zafi yayi zafi a tsakar gida suka kwana abinsu. Washe gari aka tashi da buɗar kai kenan. Tun sassafe Amare sukaita kacaniyar wanka, ƙawayen Amarya kuma ko wacce da abinda take yi dai. Cikin gida: Kukan yara da hayaniyar mata kawai kake ji. Amaryar Malam da Baba Asshi suna daga gefe suna gulma. "Malam ya sakar mata kuɗi sai wadaƙa take yi dasu. Da anyi magana Malam yace ɗanta ne mai kuɗin gidan. Kinga wata sarƙar zinare da ta saka jiya kuwa, kuma bata sa ko ɗaya daga kayan da akayi mana na fitar biki ba. Shaddoji take ta sakawa masu tsada." Cewar Baba Asshi wacce takai wuya tun sanda aka soma biki, da irin abincinnan da dangin Baba Fhatsima sukaita dafawa na alfarma dan basa ko cin abincin bikin, nasu abincin suke girkawa daban. Da kuma irin kayan ɗakin da Tasi'u yaima Hadiza ba irin na sauran yaran ba, dan hatta gara na Hadiza yafi yawa. Ga watsi da kuɗi da su Baba Fhatsima sukaita ma su Auwala, ga irin suturu da Baba Fhatsima take ta ketawa. Waɗannan abubbuwa sune suka haɗi suka tsaya ma matan Malam. Yaran gidan sai gulmar abubbuwa suke taima iyayensu mata, su kuma sai tauna lamarin suke, suna dagon maganganu masu nauyi da suke shirin fesarma Malam in an gama bikin. Baba Fhatsima: Tana tsaye cikin farar shadda da ɗan kunnen azurfa, da Ƙannenta suke maganar abinda ya dace a dafa ma baƙi. Altine tace. "Ga farfesun naman rago sukutum tun asubar fari Lamiso ta ɗaura. Wanda za a shigar ɓarayin Amare baki ɗaya. Sai ruwan shayi da burodi inaga ya isa haka. Ni batun abincin buɗar kaima zanyi miki Yaya. Anan ɓangaren naki ne za ayi yau dai biki zai ƙare?" Baba Fhatsima tace. "Yauwa Altine kinyi kyan kai, dama na fison a basu lafiyayyen kayan kari. Dangane da abincin buɗar kai matar wannan yaron Badi'a komai yana hannunta ita zata yi, abincine nasu na yaran zamani zata yi dake ba mai yawa bane, Amare kaɗai za a ɗibarma sai ƴan uwana dake ɓarayina, sai abokan Malam. Goggo Mairo tace. "Amman Yaya tun jiya Asshi take takalarmu da faɗa, sai ni nake ta daddanne Altine akan kada ta sake tayi magana. Yaron Saminu ɗazu suna alwala a ƙofar ɗakinta tana fitowa ta shiga ƙunduma musu ashariyar da duk wanda yaji yasan da iyayen yaran take yi ba dai waɗannan kuca _kucan yaran ba." Baba Fhatsima tace. "In banda ke da abinci Mairo. Ai Asshi ba zata canja ba, mai hali baya taɓa fasa halinshi. Ku dai ku yi watsin ruwan tsarki dasu, maza a tabbatar an sallami baƙi kowa ya samu Abinci. Ke Altine ki dubo mana kwanan Amare" Baba Fhatsima tana gama faɗar haka ta wuce turakar Malam. Goggo Altine ta nufi ɓarayin Amare ta dubo lafiyarau. Ko wacce tana tare da danginta, Amare anci ado, ko wacce tubarkalla kyakkyawa da'ita gwanin sha'awa. Haka dai aka gwangwaji buɗar kai, akaci aka sha harda kiɗan ƙwarya a tsakankanin matan. Zuwa bayan Isha taro ya watse gida ya rage daga baƙi sai ƴan gida. Gwadabe. Ta ɓangaren Angwaye kuma tun da suka idar da sallar isha Malam yace su sameshi a turakarshi yanason tattauna muhimmin zance dasu. Hakan kuwa akayi, suna idarwa suka je suka samu Malam a turakarshi tare da matanshi duka. Ko wanne ya nemi waje ya zauna a gefen uwarshi, abokansu kuma suka wakiltasu dan siyo tsarabar amare. "Toh Alhamdulillah an yi taro lafiya an watse lafiya, banda ƴan kunji_kunji na mata wanda ya zame musu al'ada. Ni abinda yasa na taraku a gaban iyayenku domin su zame mun shaida shine. A cikinku duk wanda ya nemi fitina ko tada tarzoma a cikin wannan gidan naku, haƙiƙatan zai fuskanci hukunci mai tsanani. Ya zame muku dole ku so junanku domin da hakanne matayenku zasu haɗe kawunansu ayi zaman lafiya. Matsawar matayenku suka fahimnci a tsakaninku ƙiyayya da rashin jituwane. To suma fa ba zasu taɓa haɗe kawunansu ba. In kuma basu haɗe kawunansu su ba, to haka zaku hayayyafa yaranku su taso babu jituwa a tsakaninsu, kamar yadda iyayenku su ka yi. Domin sune ummul aba'isin ɓata komai. So nake in gyara gidana dan gudun barin baya da ƙurar da in ta tashi ba a san adadin mutanan da zata tule musu idanu ba. Ku zaunar da matayenku ku fahimtar dasu mahimmancin ƴan uwansu. Ku umarcesu da zaunawa da kowa Lafiya. Tasi'u da Jamilu sun isheku a matsayin uwa da uba. Duk abinda ya taso ku sanar musu, zasu maganceshi sai in yafi ƙarfinsu sai mu ji a cikin gidan. Ina fatan kun fahimceni, kun gane inda nasa gaba ko?" Sabitu ne ya kalli Hannafi Wanshi, suka taɓe bakinsu carab a kan idanun Baba Fhatsima. Baba Asshi da Amaryar Malam da suka samu haɗewar kai a bikinnan suma suka wani ɓata fuskarsu. Itako Suwaiba sai kallon Malam take yi bakinta cike da abu faɗe. "Fhatsima kece Babba da akwai abinda zaki ce ma yaran naki a gurguje?" Buɗar bakin Suwaiba ta katse Malam ta hanyar cewa. "Ai daka barsu Malam sun tafi abokansu suna jiransu, karfe kusan tara saura ai ya kamata su tafi ga iyalinsu. Duk abinda zamu ce ai mun riga mun faɗa musu tun ba yanzu ba. Ko ba gaskiya ba, Asshi, Amaryar Malam?" Ta tambayi su Baba Asshi da suka ji daɗin katse Malam da Suwaiba tayi. Su Gwadabe kuwa sai sunkiyar da kansu suka yi ƙasa dan yanda tayi maganar ba daidai bane ace tayi ma Malam a gaban yaranshi ba, domin Malam ya haifi waɗanda suka girme mata nesa ba kusa ba. Itako Amaryar Malam tace. "Sosai kuwa Suwaiba. Ai duk wani huɗuba mun riga da mun yima yaranmu Malam. Itama Fhatsima tayi ma yaranta a ɗaki, sai nake ganin ba dole bane sai ta haɗesu duka an ƙara ɓata musu lokaci ba." Auwala da yake jin kamar dama ya kashe Amaryar Malam ya ɗago yana mata wani irin muzurai na ɓacin rai. Baba Fhatsima ce ta dubeshi ta tausheshi da idanunta, dan ta fahimci matan Malam ransu a ɓace yake da Malam ne akan ɗinkewarsu da tafiyarsu umara. Malam kamar ruwa ya cinyeshi haka yayi tsit. Ji yake kamar ƙasa ta tsage ya shige dan tsantsar kunyar da matanshi suka bashi a gaban yaran nashi. Da ƙyar da siɗin goshi ya yaƙi zuchiyarshi ya dubi Baba Fhatsima a karo na barkate. "Me zaki ce Fhatsima ko kuwa kin basu izinin tafiyar kema?" Ganin ɓacin rai maɗaukaki a fuskarshi da muryarshi yasa tace. "Abinda zan ɗaura muku akan abinda Malam ya faɗa daya ne. Kuyi ƙoƙarin ginin fondisho me kyau ga iyalinku dan gudun dana sanin data kasance ƙyayya maras amfani. Sannan ku sani hannu ɗaya baya ɗaukar jinka. Zanso ku kasance tsintsiya ɗaya. Banda tuna baya, gani ga wane akace ya ishi wane tsoron Allah. Ku je Allah yayi muku Albarka " Da Ameen su Gwadabe suka amsa, bacin su sauran yaran babu wanda yace uffan. Fuu suka fice, iyayen nasu suna a mugun fusace suka miƙe. Malam: "Ku dawo ku zauna ban sallameku ba" Malam ya faɗa da muryar da babu wanda yasan cewa shine mallakinta. Duk sai da suka tsorata da irin yanda Malam yake zurga_zurga a filin falon. Duk suna tsaye harda Baba Fhatsima wacce ta miƙe yanzu. Sarautar Allah suka zubama idanu. Malam baice komai ba, bashi da niyyar cewa uffan, sai kai mari da gwauro yake yi. Cikin ɗaga murya gami da tsawa_tsawa ya soma Magana. "Ashe rainin da ku kai mun ya kai ku mun diban albarka a gaban ƴaƴana? Ashe rashin ɗaukata ba a bakin komai da kuke yi ba ya kai haka? Ashe ni bazan faɗa ku ji ba? Kaiconka Magaji da son ƙyale ƙyale yasa ka auroma diyoyinka iyaye maras tarbiyya. Allah na tuba ka yafe mun kura kuraina ya Allah. Suwaiba dake da Maman Inusa ( Amaryar malam) kuje gidan iyayenku har sai na nemeku" Kalmar data girgiza hanta da huhun matan Malam. Da sauri Baba Fhatsima tace." "Kar kayi haka Malam. In hankali ya gushe hankali ake turawa ya nemoshi. Me yasa zaka sallamesu alhalin gidan cike yake da jama'ar biki, ɗakunansu ma a cike yake da dangi na nesa. Kaima Allah ka yi haƙuri" Malam ya dubeta yace" "Ki barsu su tafi Fhatsima. Bazan laminci rashin ɗa a ga ko wacce mace a cikin gidannan ba. A tunaninsu damar da suka samu a baya zasu sameta yanzu ne? Ina ba wannan magajin da suka sani bane" Su Suwaiba dai jikin tatsaure yayi la'asar. Abun kunya ne ace yanda ta aurar da yara, yau a wayi gari wai malam ya korata gida. Itako Amaryar Malam kab danginta sun san itace tauraruwar gidan malam, yau sai ace a gabansu Malam yace ta tafi gida wannan abun kunya dame yayi kama?" "Malam kaima Allah ka barsu su zauna a ɗakinsu" Cewar Baba Fhatsima. Baba Asshi tama rasa ta cewa kallon Baba Fhatsima kawai take yi. "Shikenan sun shiga rigar alfarmarki Fhatsima. Ku fuce ku bani waje. Ammanfa ku sani ana watsewa a gidannan. Kuma ku tattare yanaku_yanaku ku ficemun a gida, har sai zuwa lokacin dana ga dama nace ku dawo" Jikkunansu duk a mace suka fice ko tari an rasa wacce zata yi. "Malam ka sassauta ma kanka dan Allah. Kayi haƙuri abi komai a sannu, in sha Allah gidanka zai gyaru ya zama kamar ko wanne gidan dake da tsayayyen uba. Ni dai a kullum ina sake jaddada maka ka zama mai magana ɗaya tak. Rarrabe magana itace ta soma kawo rabewar kai a gidanka, ka zauna kayi tunanin yanda zaka tanƙwara matanka. Korarsu bazai zama ya kawo gyara ba, sai sake rura wutar gaba da ƙiyayya." Da sauri ya katseta da cewa ."amman aya zata ji tsoro tunda taga an taune tsakuwa ma. Fhatsima abinda ya faru a baya kuskurene, a lokacin idanuna duk sun rufe bana ji baba gani, giyar ƙuruciya da lafiya na ruɗata. Dube ni a yanzu da ƙuruciya da ƙarfin nawa ya ƙare kuma na kasance cikin damuwa da hawan jinin da ni na saima kaina domin bazan ga laifin Asshi ko Suwaiba ba, sabida ni nace ina sonsu har suka amince mun. Kije ki kwanta babu damuwa, Nagode sosai Allah yai miki albarka. Ina mai daɗa baki haƙuri a bisa kuntata miki da nayi a baya, ruɗin sheɗanne" Ɗan murmushi tayi mishi tace. "Da an taɓo maza sai kaji suna cewa ai ruɗin shaiɗanne, alhalin son zuchiya ke rufe muku idanunku, sai kun shiga matsala ku zama abun tausayi. Allah ya kyauta sai da safe" Ficewarta tayi ranta ya sosu ainun. Malam ya fama mata daɗaɗɗen mikin daya jima yana cin ƙasan zuchiyarta tsawon shekaru. Ta ga rayuwa ta shanye takaici kishiya da ɗa namiji samfur_samfur, sai da ta kasance fiye da mugiya dan baƙin jini a wajen kishiyoyi. Hawayenta taa share daidai isowarta bakin ƙofarta. Baba Asshi ta ja tsaki tace. "Fhatsima dani kike zancan ni dake shege ka fasa. Asirinki akan iya Malam zai tsaya dama shi shanyayye ne. Amman ni Asshi naci dubu wallahi sai dai ceto" Ɗan guntun murmushi Baba Fhatsima tayi. Ta tattako izuwa kusa daf da Baba Asshi. "Asshi kenan. La haula maganin mai tsafi, nasha tabara na sha yasin. Ni Fhatsima a tarbiyyar da iyayena suka bani babu zuwa wajen boka. Da biyayya ake kwace miji, ba da boka ba. Na riga nayi tasiri a rayuwar Malam tasirin da babu wata mace data isa ta kamo rabin matsayina. Ai matar fari daban take, darajarta ta musamman ce" Tana kaiwa ƙarshe ta juya ta shige ɗaki ta bar Baba Asshi cike da tunani tare da zabarin zuwan wayewar gari, domin ungulu na son komawa gidanta na tsamiya, dan tana tunanin Baba Fhatsima zata rushe mata shirin da tai ta shiryashi sama da shekaru talatin. Gwadabe: A gurjuge suna fitowa kowa ya koma cikin tawagar abokanshi. Gwadabe kuwa daga Tamu sai Bara'u ne a gefe da gefenshi. A jejjere kusan dukka suka shiga cikin gidan. Ƴan Takai dangin Amarya da su Laila suna tsakar gida suna cin tuwo sai kwasar hira akeyi. Idanu Laila ta zuba ma Gwadabe har gobe da jibi tana son Gwadabe, kuma duk da mata biyu daya aura lokaci guda baisa ta karaya ba, tana ji komai daren daɗewa haƙonta zai cimma ruwa. Gadararta tafi matan Gwadabe kyau da hasken fata sosai. Sai dai ta mance halayya da tarbiyya sune abun ado a wajen ko wanne ɗa ba kyan sura da haiba ba. "Angwaye masha Allah jibeku a jere gwanin sha'awa" Cewar Duduwa tanayi tana Dariya " Bara'u ne ya kulata suka ɗan tsokani junansu haka dai sama_ sama. Ayashe tace. "Ku shige abinku kunji" Wucewa suka yi izuwa ɗakin Hadiza, domin ta kanta za a soma itace uwar gida. Shafa ɗakinta ma cike yake dam da ƙawayenta. Da sallama suka shiga falon Amarya dake buga ƙamshin turaren wutan halut oud, da kuma ƙamshin sabon fenti da sababbin kaya. Hasana ce ta nuna musu waje a saman kujeru suka zauna. "Mun same ku lafiya, ya akaji da taro?" Suka haɗe baki wajen amsawa. Bayan haka ƴar nasiha ce ta biyo baya daga bakin Tamu da Bara'u taƙaitacciya. Nera dubu ukun Najeriya suka basu a matsayin kuɗin sallamar ƙawaye. Bara'u ya ajjiye ledar kazar da kayan shayin, su ka fita tare da ƙawayen Amarya baki ɗaya. Gwadabe dai bai yi yinƙurin rakiya ba ma. Komawa yayi da hanzari kusa da matarshi Hadiza. Ɗagowa tayi suka haɗa idani ta sakar mishi murmushi mai taushin gaske. "Barka da zuwa angona, yau dai ga Hadiza a matsayin taka kuma uwar gida a gidanka" Murmushi yayi, a lokaci guda yanayinshi ya ɗan sauya. Ƴar yarbawarshi yake tunowa da lokacin da aka rakashi ɗakinta, da daren farkonsu, da irin farin ciki da jarumtar da Iyabo ta nuna mishi. Idanu ya lumshe a hankali. "Lafiya kuwa sai naga yanayinka ya sauya. Wani abunne?" Hadiza ta tambaya a ɗan tsorace. Jin muryarta cike da damuwa yasa ya ture tunanin komai. "Babu komai Uwar gida. Wannan daren namu ne mu angwayen gidannan mai albarka. Yanzu dai mu soma da yin nafila bisa sunna, sai mu baje in ciyar dake kazar amarci. Ke kuma ki shigar dani duniyar sama jannati" Dariya tayi mishi kawai. Shi ya soma tafiya ban ɗakiin yayi alwala kafin itama ta shiga tayo nata. Yanda tsarin bayan gidan gidan yake shine, da farko in ka buɗe ƙofar farko, ɗan wani wajene kamar ƙaramin falo, kitchen da ban ɗakin suna kallon juna, sai ƙofar shiga falon tana tsakiyarsa. Ginin wajen rabi ne, kana iya ganin shigar mutum banɗaki da fitowarshi, ɗan ginine rabi, da ƙaramar ƙofa. Haka duk tsarin ginin yake. Siminti ne luwai_luwai a dandamalin kitchen da banɗakin, da ƴan ƙofofin katako dai haka. Gwadabe ya ja su Sallah raka'a biyu, tare da adda'ar samun zaman lafiya, zuriya dayyiba. Daga nan suka ɗan taɓa ciye_ciyen kaji da madarar shanu. Gaga_gaga Gwadabe ya soma raba Hadiza da kunyarta, cikin salon dabara da hikima Gwadabe ya samu nishaɗi da farin ciki da nutsuwa a wannan dare mai albarka. Masoyan suka cakuɗe suka zama abu guda, zukata suka cika da sabon shauƙin juna. Cikin wannan shauƙi bacci yai awon gaba dasu izuwa kiran sallar assalatu. A mugun gajiye tulus Hadiza ta tashi zaune, doguwar rigarta ta hango a wancakale kusa da sib, jawo rigar tayi da ƙafarta ta zura kafin ta miƙe. Ashe Gwadabe idanunshi biyu ita yake kallo, har ta sa kai zata fita yace. "Ina zaki je?" Juyowa tayi tana kallonshi magashiyan a kwance, hasken lantarki na haske shi. "Dama zan kunna risho ne in ɗuma mana ruwan zafi" Miƙewa yayi tsaye. Tayi saurin kawar da kanta, abinda ya ankarar dashi kenan. Sai ya suturta kanshi ta hanyar gajeren wando. "Basshi da zafinnan zai fi kyau in watsa na sanyi. Sai dai in kece kike buƙatar ruwan zafij ko? Ya ɗan kashe mata idanu" A tsaye ya wuce ya barta tana murmushi. Bayan gida ya shigeta kuma ta shige kitchen. Tana jiyo ɓuruntu a ragowar kitchen ɗin Amaren gidan. Ɗakin Sabitu dake kallon nasu ma, ta hango shigar Sabitu bayi, buɗe ƙofar falon da yayi ne hasken lantarki yasa ta hangoshi. A gurguje Gwadabe ya fito. Kayanshi ya mayar ya fice masallaci kasancewar bai ɗakko boron kayanshi ba. Fitarshi Hadiza itama tayo wankanta a gurguje ta shige ɗaki. Duk yadda taso kar a ganta sai da Sabitu da Matarshi suka ganta. Sallar asuba ta gabatar bacci sai ɗebeta yake yi. Murmushi tayi sanda ta tuno abubbuwan da suka wakana a daren jiya. Wata sabuwar rayuwa a jiyan Gwadabe ya shigar da'ita. Yau ne ta tantance tsakanin namiji da mata maza. Dan tsohon mijinta irin ƴan ƙauyannanne da basu iya tura ƴan aike kafin zuwansu ga iyalansu ba. Salamatu kwanta kawai ta sani ita, domin dashi aka raineta. Amman yau taji daɗi da garɗin da ƙawayenta ke yawan bata labari. ( Khadija maidoki)Sib ɗinta ta buɗe ta ciro wata gorar magani, data ɗaga kai sai da ta sha rabi kafin ta mayar. Tana mayarwa Gwadabe yayo sallama ya shigo fuskarshi yalwace da fara'a da ƙyallin man angwanci raɗau a fuskarshi. Kusa da'ita ya ƙarasa ya riƙe hannayenta duka biyu. Baice mata komai ba sai kallo da yake ƙare mata. Haƙoranta biyu da suke ɗan fitowa waje yake kallo. Shi a idanunshi ba matsala bane, sai dai a idanun mutane. Tsarin zubin fuskarta ya ɓoye wannan nakasun haƙoran nata. MRS BUKHARI Ce [06/08, 9:35 am] BADI'AT IBRAHIM: *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 [15/08, 8:00 am] BADI'AT IBRAHIM: Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 ZEE MUSA COLLECTION 💃🏼💃🏼 Tana siyarda atamfofi da laces da shaddar da sauran kayan Yara da shoes and bags da material zee Musa collection ba, anan ta tsaya ba tana siyarda kayan kitchen da supplement da saurankayayakin masu inganci kaidai ka garzaya 🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️Kar ayi Babu Kai ko ka tuntibeta ta wannan number din kamar📞📞08029882667 nagodee 💃🏼💃🏼💃🏼 [8/24, 8:56 AM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 13 Sannan ga wani irin ƙunci daya aureni ko da yaushe saina zubar da hawaye. Zuchiyata ɗaci take yi mun ainun. Nayi iya yina dan ganin nabar wannan gidan aikin. Wallahi abun yaci tura, sunƙi saurarata fu, sai suturu da ɗan kuɗi suke bani. Dan a zahiri basu da matsala barsu dai da fi'ili irinna tsofaffi. Haka na share wata huɗu, a lokacin harna fidda ran barin gidan, na kuma san Uwani ta riga da ta tafi Najeriya ta huta abunta. Sai fa in keɓe kaina inta aikin kuka. Ana haka tsohuwar da nake ma aiki tazo ta sameni a kitchen tace in haɗa kayana zata kaini wani gidan in zauna zasu tafi yawon buɗe idanu ƙasashen turawa wata biyu zasu yi. Na dubeta na ɗan cakuɗa mata larabcin ina nunar mata ta mayar dani can inda ta ɗakkoni ni Najeriya zani. Ai nan ta shiga faɗa tana zagina. Shine take faɗamun Hajiya ce tace karta barni in sake komawa gidan, ta siyar dani sun biyata kuɗina dan haka na zama baiwarsu wacce suke da iko da'ita. Kunji wata ƴar duma_dumar fitina. Wasu zafafan hawayene suka gangaro a kumatuna take na soma ambaton Allah. Na kwashe kayana tsab na bi bayansu. Ina bayan mota a zaune ina ambaton Allah. Gabana yanata tsananta faɗuwa dai haka. To da safe ne lokacin, amman bamu muka isa ɗan ƙauyannan ba sai wajajen sha ɗayan dare. Wani ƙauyene me kyau muk iso, gasu da awaki masu ƙoshi da buzu buzun gashi. Wani gidan laka muka shiga, ta cikin gidan me kyau an ƙawatashi da abubbuwan gargajiya masu ƙawa. Babban falon gidan wata iriyar kujerar larabawace wacce babu katako, kamar fulo take irin manyannan da bango ake jinginata. Da wasu riɗa_riɗan Mata naci karo suna zazzaune. Sai naga wata baƙar yarinya a cinyar wata balarabiya. Yarinyar zata kai shekaru sha takwas haka, da na ɗauka ƴar Najeriya ce, ashe irin baƙaƙen kenya ne. Gata da buɗaɗɗen idanu. Abinda ya tsoratani yarinya babu kaya a jikinta daga ita sai ɗan diras da rigar nono, shigowarmu ne balarabiyar ta cire hannunta daga rigar maman yarinyar. Sai naji duk na ruɗe hankalina ya tashi ainun. Nan duk suka miƙe suna ma iyayen gidana sannu da zuwa. Ɗaya daga cikin matan ta nuna mun wajen zama, na ɗan dofana jikina. Madara aka kawo mana da romon nama babu magi sai warin tafarkuwa kawai. In da sabo na saba da wannan cima. Ni dai dan tsoro nace na ƙoshi. Iyayen gidana suka ɗan taɓa dai haka, kana suka fice abinsu.Ɗaya daga cikin larabawan sai ta mun maganar kurame tana mun nuni da in ɗakko kayana muje ta kaini ɗaki. Na bi bayanta zungui_zungui har zuwa wani ɗaki madaiaici da gado, harda durowar ajjiye kaya me kyau. Da larabci tace dani. "Wannan shine ɗakin ki da safe zan zaga dake kiga aiyukan da zaki dinga yi. Zamu biyaki sosai. Kuma zamu siyo miki kayan sawa bama son ƙazanta muna yawan yin baƙi sannan bama son hijabi, iyakarki dashi Sallah, irin wannan kayan zaki dinga sawa." Ta nuna mun zatinta. Gajeren wandone mai kwalliyar tsagu hagu da dama, sai ficiciyar rigarshi ko hannu babu duka mamanta a waje fa suke. A daren ranar na shiga damuwa mai tarin yawa. Bayan na rama sallolina ina zaune ina roƙon Allah sai ga wannan baiwar Allah ta shigo. "Ga kaya ki saka, saiki sameni a falo, zan Kai ki kitchen ki dafa ma baƙinmu Shayi" Kai na gyaɗa mata kaina kawai. A lokacin ɗaya na dare zata yi. Ban ɗaki na shiga nayi wanka na fito. Ina buɗe kayan sai naga wata yaloluwar riga gajera mai hannun shimi sai hular gashi. Na juya rigarnan yafi sau a ƙirga, da ƙyar na saka yadda ta fitomun da zatina sai naji kunya du ta kamani rigar ta matseni ainun iyakarta kuma guiwa. Ina tsaye wannan balarabiya ta shigo. Nayi sauri na kifa wannan hular gashi a kaina. Takowa tayi kusa dani tana ƙamshi cikin harshen larabci tace. "Kinyi kyau ƴar aiki. Dole a haka zaki dinga aiki a gidannan. Wuce muje in nuna miki kitchen" sim_ sim_ sim nabi bayanta har zuwa kitchen. Kayan shayin da kofuna duk dai ta nuna mun duk yadda zanyi. Na ɗaura shayin sai na soma wanke_wanke dan naga uban wanke_wanken dake kitchen ɗin sai naji gara in yishi in rage aikina na gobe. Shayi ya dahu na zuba a wata ƙatuwar buta mai kofuna guda sha biyu harda tiranta. Na ɗauka ina tafe ina harɗewa gabana sai faɗuwa yake yi. Tun kafin in ƙarasa falon nakejin waƙar larabawa na tashi, ga ihun mata inaji. Na jima a tsaye ina tunanin taya zan ratsa cikin mutane a haka. Ina hawaye na shiga. Kutsa kan da zanyi naga mata cike da falon. Wasu suna tsaye sunata rawa, kuma fa daga su sai rigar mama da ɗan diras masu wasu wawalniya sai rawar ƙugu suke yi. Wasu kuma suna zaune a kujeru suna ta shafar jikin junansu. Wani tashin hankali da na gani anayi, wallahi ba shiri na dire tiran shayin na zura a guje sai ɗakina. Na fige hular gashinnan na durƙusa ina kukan tashin hankali. A fusace naji an buɗe ƙofar ɗakin, wannan dai wacce ta bani kayane. Cikin zafin nama ta zabgamun mari ashe wai na fasa kofi ajjiye tirannan da nayi da ƙarfi. Ta dinga zagina tana mun barazana masu nauyiin faɗe. Haka ta figeni bata sakeni ba sai a tsaƙiyar falonnan. Jikina na rawa na dinga binsu da shayi, wasu su ɗauka, wasu su ɗaga mun hannu. Kunji wata ƙaddara kuma. Dana dinga aikin dafa shayi sai wajajen ukun dare suka barni naje na kwanta. Idona ƙyam kamar an soya gyaɗa. Abubbuwan da naga mata nayi a tsakankanin junansu ne ya tsaya mun daram a raina. Kenan nan gidan ƴan maɗigone, ko gidan karuwaine aka kawoni? Ni dai cikina ya ɗuri ruwa, akan sallaya na kwana ina roƙon Allah ya kareni. Da asuba inayin Sallah na tsiri aikin gidan ko ina kaca_kaca. Sai kwashe rigunan Mama da ɗan diras nake. Na samu leda na tattare na gyara ko'ina na tsabtace komai, wajajen sha ɗayan rana na dafa tea na haɗa da biredi na karya. Har wannan lokacin babu wanda ya fito ni kaɗai naketa ɓuruntuna, sai wata ƙatuwar mage da take ta guje gujemta ita kaɗai. Bayin Allah'annan basu suka fito ba sai wajajen ƙarfe biyu da rabi na rana. Mutum biyu suka zauna, sauran huɗun suna tsaye sunyi shigar banzar data wuce ƙa'ida sai suka ɗaura abaya a saman kayan. "Zamu fita, kafin mu dawo kiyi abinci, kuma ki gyara mana ɗaki, wanki ma duk yananan mun tara" Cewar ɗaya daga cikin matan da naji ana kiranta Basma. Da harshen larabci take maganar. Tana dasa aya suka fice. Biyun dake zaune a kujera suna kallon wani shiri na batsa suka ce in haɗo musu Karin kumallo. Da sauri na fita, matane a cikin akwatin talabijin ɗin sirara suna rawa. Ni dai ina hawaye na dafo musu shayi na turara musu gurasa na kai musu. Ɗakunan kwanansu na wuce, nan na shiga aiki ka'in da na'in dan Komai a zaune yake daram, ni na kintsa komai. Na buɗe sib duk na hallage musu dogayen rugunansu. Ina wannan aikin fa na kunna injin wanki ina wankewa ina busarwa. Sai la'asar na kammala. Ba zama na soma guga, ga girki ina tashi ina dubawa, kafin magriba dai na gama komai, da nayi Sallah sai na ɗan kwanta. Gabɓaina babu inda baya nishin ciwo. Ƙofar ɗakin aka turo da ƙarfi. Idanuna na sauke ganin irin kallon maitar da take yi mun tamkar mage taga ɗanyen kifi. A hankali take takowa duk takunta sai inji gabana ya sake tsananta bugawa. " Anti jamilatun wallah, A ti hibbina ni? ( Kina da kyau wallahi kina sona?) Kalmar sai naji tayi mun wani gingingin a kaina, tunda nake ban taɓa tunanin mace zata iya irin wannan muryar mai kashe jiki ga ƴar uwarta mace ba. Ɗan manuniyarta ta ɗora a wuyana tana mun tafiyar tsutsa izuwa wushiryar data raba mamana. "Ma qulti shai'an Jamilatun? ( Baki ce komai ba) "A ti hibbina ni? ( Kina sona) Ta sake maimaitamun. Ni dai na kasa furta dai_dai da kalma, jikina ya mutu tuɓis rokon Allah da nadamar baro ƙasata ta gado ya sake ɗarsuwa a zuchiyata, tsanar wannan mata sai ninka kanshi da kanshi yake yi. " Khus mala bi si ki ( Karɓi kayanki) Ta miƙo mun babbar ledar dake hannunta. Nasa hannu cikin ƙosawa na amsa. Shukran jazilan ( Nagode sosai) Iyakar abinda na faɗa kenan, harta kai bakin ƙofa tace. "Ismi Kariya" ( Sunana Kariya) Sai ta fice, na saki wawuyar ajjiyar zuchiya. Na kasa tsaye na kasa zaune, da dai naga babu sarki sai Allah saina fita falo da zummar zuwa kitchen ɗakko abincina. Da wannan riga fa iya guiwa da aka bani fa kar ku mance duk nake wannan zurunkaɗanar. Ina shiga falon naga Kariya da Aliya suna aikata ɓarna. Gyaran Murya nayi musu, ko a jikinsu ina waige harna isa kitchen. Tsabaragen takaici a kitchen ɗin nayi zamana naci abincin wallahi nayi kwanciyata a kan tayil a wajen na kwana bani na farka ba sai asuba. Nan ciwon bayana fa ya tashi kunsan sanyi yanda yake tada ciwukan ƙashi ( khadija maidoki wai sanyi na tada ciwukan ƙashi?) A taƙaice sai Aliya ce ta taimaka mun na iya miƙewa, Sallah sai a zaune nayi ta. Ranar dai banyi aiki ba sai washe gari da na ɗanji dama_dama. Haka rayuwata taci gaba da gudana cikin wannan kazanta da tashin hankali. Babu irin abinda ni Iyabo idanuna basu gane mun ba. Suturar banza ni kaina dole haka nake sanyawa inta hidimar aikina a hakan. Allah ya ga zuchiyata ba"a son raina bane. Tsorona Allah tsorona kar in gudu in faɗa mummunan hali, amman wallahi da zan gudu, kuma ina tunanin Uwani ko tana can tana jirana kota koma najeriya ne, duk ban sani ba. Babu rana mafi muni da tashin hankali data wuce ranar da Kariya ta zo ɗakina cikin dare da burin kasancewa tare dani. Dama ta jima tana tattaɓani haka tana bani kuɗi. Tayi tayi in saki jiikina da'ita amman Allah yana kuɓutar dani daga sharrinta. Sakamakon adda'a dana tsananta yi babu dare babu rana, cikin Sallah ko cikin aikin bautar da nake yi babu lokacin da adda'a take barin bakina. Ina kwance akan sallaya bayan na gama ƙiyamul laili, sai naji kamar a mafarki ana rabani da suturuna dai haka. Kasancewar jikina ko da yaushe a tsamane yake da kafirar gajiya, dole baccina zai kasance mai nauyi, kuma dama bana yi ma da wuri shi baccin. Wallah duk abubuwa da sukaita wakana cikin mafarkina nake jinsu a nawa wautar. Ashe a zahirance suke faruwa dani ni Iyabo. Dare mafi baƙi a gareni, jin hannu da bakin Kariya a inda bai dace ba shi ya dawo dani na kasance a farke. Kaina yaso tarwatsewa baki ɗaya ma. Wuƙa ta zaro a rigar Mamanta ƴar ƙarama, sai kawai ta tsaga mun gefen fuskata. Ko zafi banji ba, dan tafasar da zuchiyata take yi kan abinda take aikatawa dani yafi mun zafi, fiye da yankan wuƙar. "Bana so kice komai. In kika yi yinƙurin yi mun gaddama kasheki zanyi in tona rami in burneki a gona. Kibi umarnina in ƴantaki" To a gaskiya na tsorata da kalamin Kariya, kuma ba barazanace take yi mun ba da gaske take nufin zata kasheni. Maganganun Faty ne suka dawo kaina da labarin yanda wasu daga zuwa gidan aiki ba a sake jin ɗuriyarsu har abada, sai dai iyayensu dake gida najeriya suji shiru. Idanuna a runtse harta gama komai. Kuma abu mafi wahala da ɗaga hankali shine umartata da tayi kan in yi mata sak abubuwan da tayi mun. Naso in turje, sai tayi sauri ta zaro wuƙarnan ta sake kawo mun yanka. Cikin zafin nama na kauce. Babu shiri na soma yi mata abinda take so. Allah ya ga zuchiyata ina mai ƙyamatar dukkan abinda nayi ma Kariya, da dukkan wanda tayi mun. Tun daga wannan rana saina samu rangwame, yawan aiki sai ya ragu mun. Ni dai a kullum ina roƙon Allah akan ya kawo mun mafita, ya kuɓutar dani daga wannan rayuwa baƙa. Nan fa gaga _gaga al"amura suka ci gaba da tafiya a baibai, har wata biyu ta cika. Sai na ke tambayar Kariya yaushe iyayen gidana zasu zo su ɗaukeni ne?. A lokacin muna banɗaki inai mata wanka. Buɗar bakinta sai cewa tayi. "Na siye ki a hannunsu kamar yadda suka faɗa mini suma siyanki suka yi. Abinda nake so dake shine ki cire tunani da mafarkin Najeriya a ranki, ke da Najeriya har abada" Ai sai kuka, sai zazzaɓi, daga zazzaɓi sai babbar jinyar da hatta abinci sai Kariya ta bani a baki. Kuma ta kira likitansu yazo ya dubani. Sati na biyu cur idanuna kullum cikin danshi suke. Wata rana ina aiki a kitchen Kariya ta shigo take sanar dani zasu je Umara in zauna in kula da gidan. Harta juya cikin tsoro nace. Uridu an azhabu ma'akum ila Umara billah. ( Inaso in biku umara dan Allah) Ƙur ta yi mun da idanunta, da Allah ya ɗaurani a kanta sai ta amince mun. Cikin murna na sako kayan jikina na bisu. Muna tafe a mota ina kallon gari, ina lure da komai ina sassaka amala a ko wanne kallon kan titi. Tafiyar bata wasa bace, cikin amincewar ubangijina sai gani a Ka'aba har a jikinta. Kuka na fashe dashi inata roƙon Allah yafiya dan gani nake yi Allah bazai yafe mun kan ƙazantar da ake sani yi dan dole ba. Adda'a nayi na maimaita babu iyaka. Zuchiyata saita samu salama da nutsuwa yau na yi umara gani a ɗakin Allah. A hotel ɗin wajen Harami muka kwana kafin kuma muka koma gida. Naga ƴan ƙasata najeriya, nayi magana dasu na samu farin ciki. Na barbaza idanu ko Allah zaisa in ga wanda na sani a kamfaninmu amman Allah bai haɗamu ba. Amman na samu nutsuwa a zuchiyata in sha Allah na kawo kukana gindin maganin. Allah cikin ikonshi kwana biyu da dawowarmu Umara, da daddare na zage na yima Kariya abinda tafi so, sai murna da daɗi take ji, Allah sai ya matsi bakinta tace. "Zan miki duk abinda zai faranta miki. Zan iya miki komai. Da hikima nace da'ita. Inason ki kaini kamfani zan tura da kaya Najeriya akwai masu tafiya, kuma zan tura ma ƴan uwana da kuɗi" Allah mai yin yadda ya so, sai ta amince ba tare da tayi tunanin komai ba. Ni kuwa a cikin daren na haɗe kayana tsab a wani ƙaton akwati ko tsinke ban bari ba. Kuɗaɗena dama suna ɗamare a marata. Na mance ban faɗa muku ba har setin ɗan kunne da sarƙa, awarwaro, zobe, chain ɗin ƙafa Kariya ta sai mun masu darajar gaske. Washe gari sassafe ta kira uwar ɗakina wannan tsohuwa data kawoni, ita tai mata kwatancen kamfani. Ta kira wani saurayinta ya zo da mota ya kwashemu, da tarin kayana dan na samu alkhairi sosai a gidan. Tafiya muke, ni dai adda'ace kawai a bakina, gabana sai yankewa yake yana ta fa faɗuwa gani nake kamar za'a samu matsala. Tafiyace ashe bana wasa ba a gabanmu, a hanya mu ka yi azahar muka yi la'asar. Muna zaune a wani ƙauye gidan cin abinci sai ga kiran wayar Aliya. Ina jiyo duk abinda take faɗa dan a lokacin harshena na larabci yayi ƙarfi sosai. Sai hantar cikina ta soma tsittsinkewa dan tsoro, gudawa ta taru a cikina. Wani irin mugun kallo Kariya ta watsa mun bayan ta ajjiye wayar. Babu abinda nake ambato sai Allah, nasan shi ne kaɗai zai taimakeni a kan duk tsananin da zan shiga. "Me yasa kike tunanin ni zaki yaudara ki gudu?" Ta furta da harshen larabci. Sai da na ambaci Allah kafin na ɗaure fuskata nace. Na sanar dake komai tun kafin mu fito. Kaya zan tura Najeriya a ajjiyemun. Kuma a hakanma zanje in yi siyayyar kaya in haɗama wacce zata tafi duk a tafi mun dasu. Ba guduwa zanyi ba" Na ƙarashe maganar tawa da sarƙewar harshe. Ta dai nuna kamar ta gamsu da bayanina tunda har muka kama hanya. Bamu muka iso ƙofar gidan da muke ba sai wajajen 1 na dare. Muna isowa wata mota itama tana parker wa kamar tare muke. Faty ce naga ta fito a motar tana tangaɗi kamar mai jin bacci. Da sauri na ɓalle murfin motar na fito. Na sakko da bataliyar kayayyakina. Faty tana hangoni sai ta zo tana fara'a. Bansan sanda na rungumeta muka saka kuka dukanmmu ba. Ashe Saleem da saurayin Faty sun iso daf damu bamu sani ba ma. "Iyabo kice kika ƙare haka, ashe kina raye Hajiya tace kin mutu?" Murmushi nayi nace da'ita. Ban mutu ba ina raye, mummunan hannu na faɗa amman Allah ya kuɓutar dani." Ba sai na jiyo na dubi Kariya nace da'ita. Ni na dawo gida kenan babu ni ba ƙasar Saudiyya ma baki ɗaya Najeriya zan koma" Ranar naga tashin hankali dan Kariya sai ta soma daddannamun ashariya tana fincikata kan lallai sai mun koma. In ba haka ba zata kira askarawa su zo su kamani. Da rikici yaƙi ya ƙare sai Salim ya mun nuni da in koma gefe. To a lokacin har matan gidan namu sun soma fitowa. Cikin hukuncin Allah sai ga Uwani itama ta fito sai raba idanu take. Karab muka haɗa idanu mu kai ma juna murmushin farin ciki. Tana ɗingishi ta ƙaraso kusa dani muka riƙe hannun juna gam tamkar ance za a farraƙamu. Rikici fa ya kai har Hajiya ta fito. Tana ganina itama fa tace. "Baki isa ki koma mun cikin gida ba. Sai dai ki nemi inda dare yayi miki. Har ke Uwani kar wacce ta koma mun cikin gida" Tana faɗar haka sai tace da Kariya karta yarda ta tusani gaba sai mun koma" "Ku shiga mota dake da ƴar uwar taki zan kai ku gidana" Cewar Salim wanda ranshi ya gama ɓaci. Faty ce ta ja hannuna muka wuce ni kuma ina riƙe da hannun uwani dama. "Uwani bari in ɗebo miki kayanki, tunda muguwar matarnan ba barinki zata yi ki shiga ba" Faty amman dake zamu tafi ko? Ni fa tsoro nake ji, kuma wallahi Najeriya zan koma" Ƙur ta dubemu can kuma tace. "Shikenan zan biku har saina tabbatar kun tafi Najeriya sai in dawo, yanzu dai ina zuwa" Nan ta tafi ta barmu, ni ai saina haɗe kaina da guiwata na dinga dirzar kuka kamar raina zai fita, Uwani ma sai shessheƙa take yi. Kayanmu su Salim suka lode a bayan Bot, Faty ta shigo mota muka ɗauki hanya. Salim sai roƙona yake yi akan in daure in yi shiru ya'isa haka. Amman ina wani baƙin ciki da nadamar zuwa ƙasar ke turniƙeni. Duk mun lalace mun faɗa balaoi iri da kala. Tafiyar da mu ka yi bata wuce tafiyar awa ɗaya ba sai gamu a wani katafaren rusheshen gida, mai yalwar filin tsakar gida. Salim na gaba muna biye dashi a baya har zuwa cikin babban falon gidan, inda ya kasance matattarar ɗakunan gidan, da ƙafar bene da zata sada me hawa izuwa sama. Babu kowa a falon a lokacin da muka shiga. Har ya kama ƙafar benen sai ya soma kiran sunan Atika, Atika. Allahu Akbar sai ga wata ƴar burkina fasu ta tawo a guje har tana tuntuɓe jikinta da uniform na masu aiki. Yace ta haɗo shayi da abinci ta kawo mana ɗakinshi. Nan muka haura tiryan_tiryan har izuwa ɗakinshi daya kasance madaidaicin ciki da falo mai shaƙe da kayan alatu. A irin kujerarsu mai daɗin zama muka zauna duk a takure ni da Uwani Faty kuwa a cinyar saurayinta ma tayi zamanta tana yi mishi raɗa a kunne. "Ku saki jikin ku nan gidanki ne ƙawata. Ummi da Abi sun fita, gobe zan haɗaku dasu ku gaisa." Mun gode sosai Allah ya saka da Alkhairi. Faty kema babu abinda zamu ce dake sai godiya" Na faɗa jikina a sanyaye sosai. Waje saurayin Faty da Salim suka bamu, mu kai wanka muka kintsa, na rama sallolin da suke kaina. Sai ga shayi da shinkafa da romon nama Atika ta kawo mana. Bayan munci ne Faty tace. "Yaya akayi Hajiya tace damu kin mutu Iyabo?" Ɗan dariyar takaici nayi musu nacce. Sabida ta siyar dani ba. Kuma ta basu uwarnin karsu sake su barni in fita ko ƙofar gidane. Duk da inna fitan bansan inda zan dosa ba, ina tsoro da gudun faɗawa matsala" Nan na soma labarta musu baƙar wuya da azabar da na sha, da ƙazantar dana tsinci kaina a ciki na ƙarfi da yaji. Uwani ta fashe da kuka tace. "Nima haka na samu wata uwar aiki ta dinga tursasani irin ƙazantar da aka saki a ciki. Iyabo naci baƙar wuya. Kinga dama ni tunda labarin mutuwarki yazo garemu na yanke yin waya da su Hajiya, da Hafizu da yaran duka. Dan na yanke har abada bazan koma Najeriya ba. Dan bansan me zance ma danginki ba" Ina hawaye nace Sake komawa gidan aiki kika yi bayan rabuwarmu dake da nace ki bani wata ɗaya zan dawo?" "Gidajen aiki har uku ma masu mugun hatsarin gaske. Amman babu abinda zamu ce da Allah sai godiya. In sha Allah daga nan sai gida Najeriya. Kuma na gode Allah nayi Umara har sau biyu. Kefa kin samu wannan damar?" Ta tambayeni da karshashiin son jin amsa. Idanu na lumshe na buɗe. Na samu damar yi sau ɗaya. Alhamdulillah. Bani da burin daya wuce in sa iyayena da yarana a idanuna. Nifa tunda nazo ƙasarnan sau ɗaya tak nayi wayaa da Burodami Debisi " Faty tace. "Ai kuwa wani mai suna hakan ya kikkira wayata. Sai wani mayen Hamma da duk bayan kwana biyu sai ya kira wayata yanaso yayi magana dake" Idanuna na lumshe soyayya da kewar Yaya Hamma suka dirarmun a zuchiyata farin ciki ya kamani. To ku aramun waya in kirasu. Allah sarki Yaya Hamma ɗan amana ashe ina ranshi kamar yadda shima yake raina" Faty ta miƙo mun wayarta tana daga kwance. "Banyi serving number shi debisin ba. Amman na seving ɗin ta Hamma guda ɗaya. Dan lambobi daban_ daban yake kira dasu. Daga baya ne yace in save ɗin wannan, in kin zo in baki shine layinshi. To shine dawowar da baki yi ba sai yau" MRS BUKHARI 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 [8/24, 9:22 AM] +234 806 803 9890: NAMA YA DAHU..... ROMO ƊANYE BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI GAWURTATTU UKU 12 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. Number na dana saka a jikin littafi ya sake tono mun masoyana masu son magana dani sosai. Daga ranar dana saka numberna izuwa yanzu wlh bazan iya ƙirga adadin saƙonnin dana riske ba. Babu abinda zance da masoya sai godiya. Hakan ya sake fallasa ƴan bati suma, son so 😀👍🏻 IYABO: Ina kan sallaya hannu da kaina a sama ina roƙon Allah ya kawo mun sanadin komawata ƙasata najeriya kar in mutu a wulaƙance a inda rayuwata bata da amfani. Yaya Hamma na tuno da ƙoƙarin da yayi akaina domin in haƙura da tafiyar naƙi. Haka zalika Burodami Debisi yayi ƙoƙarin hanani tafiyarnan idanuna sun bushe gani nake tafiyar itace mafita. Ashe rabon shan wahala ne, ko da wannan ciwon bayan aka barni ai na horu. Fati ce ta shigo ita da Sima ɗan daudun ƙawarta. waya take yi sai larabci take yi, wasu zantukan ina fahimtar me take cewa wasu kuma bana ganewa. Na fahimci da namiji take magana, kuma maganar haɗuwa suke yi. Data ajjiye wayar sai na dubeeta nace. Faty na lura kamar mu,amala da maza shine sana'arki ko?" Na ƙura mata idanu ina karantar yanayinta. Sima ya tafa hannaye yace. "Yau ni naga jar jaraba ido da ido, Iyabo kike ko wa?" Ni dai ban tanka shi ba. Ido cikin ido tace Faty tace." "Ƙwarai da aniya. Jikina shine jarine, babu kasuwanci mai ci a ƙasarnan sama da wannan. Kema kuma dama ce da zaki tara kuɗaɗen da ko kin koma Najeriya ba kiy babu talauci. Kin ganni ina da gidajen da ake mun haya. Mijin da zan aura dawowata kawai yake jira. Na tuttura dilolin kayayyaki gida Najeriya dana koma nima na zama daga cikin waɗanda za a dama dani, hatta kayan kitchen ɗina da kayan ƙyale_ƙyalenmu na mata duk nayi ma kaina. Hmmm Iyabo nima da wanke_wanken na soma. So uku ina zubar da ciki a wannan ƙasa, na farko yaron gidan aikinane yai mun ciki, na biyu Ya Babana ne yai mun ciki ( Ya Baba kamar uban gida ake nufi). Na ukun abokin yaron gidan aikina da yaro daga Canada yai mun ciki. Wuya babu irin wacce ban sha ba a gidan aiki. Wasu fa har rasa rayukansu suke yi. Kema in baki haƙura da gidan aiki ba, wallahi sai aikin gidan larabawa ya nakasa miki jiki, baga irinta nan ba, ciwon baya ya soma kama ki ba, duk da ciwon bayannan suke komawa najeriya su zamema danginsu layabiliti. Tun kafin ki rasa lafiyar ƙafafu a mayar dake Najeriya hajaran majaran ba lafiya ki zame musu nauyi, ke baki tara kuɗi ba, su ki cinye musu nasu gara ki haƙura da wannan aikin." Wani zumm naji a jikina tamkar an jona mun shokin wallahi. A dibibice nace. Duk a gidan aikin kika haɗu da wannan ƙaddarar? Amman Faty me yasa baki koma Najeriya ba? Wannan rayuwar ai ba mai ɓullewa bace, babu yadda za ayi ka saɓi Allah kuma kaga haske a gaba. Ni dai da in bi maza gara in koma Najeriya a nakashe, ke koma in mutu, sai dai ai mun da ƙarfin tsiya. Kema ina mai baki shawarar ki tuba, daga ke har Sima" Hawayene ya zubo a idanunta sai girgiza kai take yi. Sima kuwa dariya da wata girgiza yayi ya bude jakarshi ya zaro hanbaki mai ruwan toka ya sake shafawa. Kullum bakinshi da wannan janbaki kamar akuya ta dumbuji gari. Faty ce kawai tace. "Ni zanfita sai gobe zan dawo. Ƙila in na dawo in tsokata miki kaɗan daga cikin rayuwata. Zaki fahimci neman kuɗi ya wajaba a gareni. Karki mance ina binki kuɗin abinci. Akwai laban da cake in zaki ci gasu can" Ta nuna mun inda cake ɗin yake da bakinta ta fuce abunta Sima na biye da'ita. Ajjiyar zuchiya kawai na sauke, haka na kwana ina tubka da warwarar tunani, hankalina tuni ya daɗe da komawa gida. Sai kuma inna tuno da irin rayuwar da Dadana take yi a gidan azzalumin mijinta sai inji na ɗan samu ƙwarin guiwar zama in nemi kuɗi da GUMIN HALAL ( BATUL MAMMAN) In na tuno baƙar azabar aikin gidan larabawa da furucin ire irensu Faty sai inji zuchiyata ma ta tsinke. Washe gari da safe sai ga Hajiya ta leƙo dakin. Wani kallon wulaƙanci ta watso mun. "Ina dai fatan ba kin dawo bane da zummar kinbar gidan aikin ki ba ko? Dan ƴan gidan aikin ki sun kira suna tambayar yaushe zaki dawo. A tsorace nace da'ita. Bani da lafiya ne shi yasa na dawo. Da zaran jikina ya warware zan koma kan aikina" "Ya dai fi miki. Me yake damunki da baki iya zuwa mun gaisa ba?" Na kwashe labarin yadda nake ji na bata. Abun mamaki sai ta kwashe da dariya harda buga ƙafarta. Lokaci guda kuma sai ta saki tsaki tare da cewa. "Aikin banza. Da wai me kuka ɗauka, da kun shigo ƙasar kun zama masu arziki ko me? Hatta karuwan cikin gidannan da kike ji da gani suna shan wuya. Ki tambayi tantiriyar ƴar barikin data baki mafaka zata baki labarin da yadda ta soma. Ko da yake ƙila nemanki take yi ko shi yasa ma ta ajjiyeki" Tana gama faɗar haka ta saki labulen ɗakin ta barni ina shurɓune majina. Da ƙyar na miƙe a daddafe na gyara ɗakin, bayan naci kukana na ƙoshi na gode ma Allah. Baya da ƙafafu sun matsa mun, ban ɗaki na shiga na ɗan gargasa jikina da tawul, na shafe jikina tas da man zafi. Sai na ɗan bibbi bango na fita domin in samar ma cikina ɗan abun da zanci. Fitata ke da wuya, sai ga wata ƴar matashiyar budurwar da ba zata haura shekaru goma sha bakwai, sha takwas ba. Idanunta a kumbure bakinta da hancinta sai jini da majina da yawu ke dalala. Faɗi take. "Ku taimakeni bana gani. Mutuwa zanyi. Na roƙe ku ku mayar dani ƙasata najeriya na gaji da wannan azabar." Yib sai ta runtuma a ƙasa take sai ba numfashi. Hankalinmu ya tashi ainun duk muka rufu a kanta masu kuka nayi, masu salati nayi, masu cewa a kira gidansu a sanar musu halin da take suna yi. Ni dai ruwa na nemo na sheƙa mata sai ta sauke ajjiyar zuchiya ashe suma tayi. Tiri_tiri kuma suka jata zuwa ɗakinta dai. Yarinyarnan ashe gidan da take aikine, mijin matar ke kwanciya da'ita shine matar ta kamasu cikin dare. Shine tai mata irin wannan kafirin dukan. Ita ko Hajiya dawa Allah ya haɗata bayan mu. Ashe duk haya_hayar da muke yi tana. Ɗakinta bacci take yi. Tana tashi ta dira a wuyanmu ta inda ta tsikara ba tanan take ja ba. Duk mu kai tsit kowacce tayi tsamo_tsamo. Muna cikin haka yara da manyan da suka mayar da kansu fasiƙai dan cimma buri, huɗu daga cikin waɗanda suka fita kwanan gida suka shigo, ciki harda Faty da Sima. Shigowarsu ce yasa Hajiya ta sarara mana. Abinci na siya tuwo miyar kuka mai tsadar gaske. Komai fa akwai na gida najeriya takari ke siya, akwai maza da mata takari sosai, to su suke sayen wannan abinci. Su kansu masu abincinnan Hajiyoyin kansu ne in suka dawo gida Najeriya. Ina zaune ina cin tuwona, na dulmiya tunanin ko a wanne hali Dada take oho. Sai naji maganar Faty. Ɗagowa nayi ina lashe hannuna ina kallonta du a lokaci guda " "Nace zan ɗan tsokata miki labarina. Amman a dunƙule zan baki" Ajjiyar zuchiya na sauke nannauya. Ina jinki Faty. Nace da'ita tare da bata hankalina baki ɗaya. Tsulum Sima ya shige banɗaki da ɗaurin ƙirji yanata yauƙi. "Mahaifina mai auri saki ne. A iyakar tasowata matan da mahaifina ya aura sunfi ashirin. Yara a gidanmu kuwa kamar bakin masallacin juma'a. Rashin tasowarmu da iyayenmu Mata, sai ya gurɓata rayuwarmu musamman mu matan. Sai mu fita a lokacin da muke so. Ke in kwana bakwai zaki yi bakya gida babu mai tambayar dalili. Ba lalle ne ma a lura bakya nan ɗin ba. Yawo na dinga yi kwararo_kwararo domin samun na abinci da suturar arziki a matsayina na matashiya. Tun tasowata na riga na saba da kula da kaina a matsayina na mace, Babanmu iyakar abinci kaɗai yake iya bamu, shima sau biyu kuma marar daɗi. A shekara sau ɗaya rak yake mana sutura kala ɗaya rak. Ke zaki sai sabulun wanka dana wanki, ke zaki sai man shafawa, man goge baki, ke zaki biya kuɗin kitso, kayan kwalliya, turare. Ke komai da kika sani, ki faɗamun me zai sa ba zamu saba da kuɗi ba. Me yasa idanuwanmu ba zasu buɗe ba? Ita ko mahaifiyata tana can tana auren wani marar mutuncin yana mata gashin ƙuma. Itama bata samu kulawa ba, balle ta kula dani. Yaran data haifa acan ma a ƙarƙashinta suke ita ke ɗawainiya dasu har mijin ma. Kinji somi_somin taɓarɓarewar rayuwata. A wannan yawon ɓel_ ɓel Allah ya haɗani da wani ɗan shaye_shaye harda ƙaddarar aure da yaro ɗaya tilo. Kullum sai ya jibgeni babu ranar banza, matan banza har gadon sunnah ake shigomun dasu. Uƙuba muraratan. Ana cikin haka Allah da ikonshi sai ya sakeni akan karuwarshi, yace in musu girki ni kuma na dire nace banyi. Sai ya sake ni. Na tattare kayana na koma wannan rayuwa ta gidanmu, ko da aka ganni a gida babu wanda yace dani ƙala. Nima nayi banza da kowa. Gaga_gaga naita faɗi tashin neman na tuwo. Har sanadi yasa na tawo wannan ƙasa ta dalilin ƙawata. Labarin zamana a gidan Larabawa ban ɓoye miki komai ba. Naso in tuba in nutsu, amman abun yaci tura ni kuma idanuna ya bushe akan kuɗi da son ceto mahaifiyata da ƙannena da Babanmu ba ɗaya ba. Alhamdulillah yanzu su suna cikin farin ciki, kullum mahaifiyata a cikin sanyamun albarka take. Wannan shine zan iya baki a taƙaice." Girgiza kai nake ta yi, sai jujjuya labarin nake yi a ƙwaƙwalwata, ina mamakin uba irin na su Faty. Dada ce ta sake faɗi mun a raina. Amman in sha Allah da GUMIN HALAK zan kula da mahaifiyata da nawa ƙannen. Faty haƙiƙa kinga jalala." Ta ɗaya ɓangaren sai Gwadabe da yarana suka faɗo mun. Allah sarki yanzu nasan Gwadabe yayi aure, ko wanne irin hali yarana suke ciki oho. Nisawa nayi na ce. Haƙiƙa Faty kin taso a wata iriyar mummunar rayuwa. Ƙaddararki baƙar ƙaddarace. Amman fa babu wata hujja da zaki kafa domin ki saɓi Allah. Zina haramun ce, bai kamata ki kula da iyayenki da kuɗin zina ba" "Dakata Iyabo. Duk abinda kika gani a ɗakinnan, ko kika ci, hatta alfarma da nayi miki duk sanadiyyar kuɗin zinar ce. Kinga kema kuɗin yayi miki rana. Da yanzu daga ni har ke muna neman mafaka, tare da neman tudun dafawa. Jibeki fa jinyar wahala da azabar gidan Larabawa kike fama dashi. Kafin ke wasu sunyi, wasu fa tsabaragen wuya yankar jiki suke su faɗi su mutu, wasu su haɗiyi zuchiya." Da tsawa take yi mun magana yarinya ƙarama. Ko me ta tuna oho sai naji salama a muryar tata. "Iyabo tawa ƙaddararce haka. Kamar yadda ƙaddara ta zargo rayukanmu ta haɗamu a gidannan. Ki yi harkokin gabanki, ki barni inyi nawa Allah da kike ji da ganinshi me gafartama bayine." Hakane Faty Ubangiji Allah yasa mu dace. Ki taimaka ki ara mun wayarki zan kira gida. Tunda nazo ban samu damar ji daga garesu ba." Kamar dai ba zata bani ba dai. Sai ta miƙo mun. Number Burodami na lalubo a cikin kayana na kwafeta tsab a wayar na danna kore. Ruri biyu zuwa na ukun naji an ɗaga. Burodami Debisi Emi ni Iyabo ( Nice Iyabo) Ina faɗin haka sai kuka na baƙin ciki da nadama. "Ohh Ohh ohh Iyabo sai yau kika kira? Kin samu a damuwa musamman zuchiyar data shaƙu dake, ta horu da sonki. Ina fatan kina lafiya ko?" Sai kawai nace dashi. Lafiya lau, ya su Iyaa, da su Iyaa Beji da su Iya Kokodeen?" "Duk suna Lafiya. Jiya jiyannan Dada da Hamma suka koma. Sun zo kwanansu biyu. Dada ta damu da Iyaa ta faɗa mata baki kira ko sau ɗaya ba." Sababbin hawaye na matse a idanuna daɗin jin labarin Dada da Hammana ya sani cikin farin ciki. Allah sarki Dada. Suna lafiya ko? Kwanakin baya na ari waya na kiraka baka ɗaga bane. In Dada ta dawo a bata wannan lambar. Lambar yarinyar da muke ɗaki ɗaya ne. In akaci sa a na dawo hutu daga gidan aiki sai mu gaisa" Bai bani amsaba sai kuɗin ya ƙare. Kafin in ajjiye wayar sai ga kiranshi ya biyo ni. "To Iyabo zan bata. Ko bata zo ba zan shirya in an kwana biyu in kai mata. In naje gida zan kira in haɗaki da Iyaa. Kullum sai ta yi zancanki." Murmushi nayi nace. To Shikenan Burodami. Nagode, sannan a taya mu da adda'a. A faɗa ma Iyaa da Dada ina buƙatar adda'a" Buɗar bakinshi sai yace. "Masoyinki kuma mijinki na biyu ma zai hana idanunshi bacci wajen yi miki adda'a. Ina ɗan birri ɗan ƙauye me kiwo ba yamun ƙwacen masoyiya ba. In banda so da abinshi, me yasa zai kai kanshi dokar dajin da babu komai cikinta sai nono da fura" Ƙit sai na kashe wayarnan, raina ya ɓaci ainun. Miƙama Faty wayarta nayi, tare da yi mata godiya. Ban ɗaki ta shige, ni kuma naci gaba da cin tuwona. Sima na tsaye yana shafa mai yana rawa. Inata nazarin maganganun Burodami Debisi. Hammana ne ya faɗo mun a raina. Ya iyali ina son Hamma so marar abin misalin da hankali zai ɗauka. Dama zuchiyata wawuyar zuchiyace bata iya son abu ba sam. Haka kuma bata iya ƙin abu ba. Fitowar Faty daga banɗakine ya katsemun tunanina. "Da badan ƙafarki na ciwo ba, ai da kin rakani kasuwa inason sayen ɗan kunnen gold." Duk da nasan ina shan azaba sai nace mata. Da yaushe zaki je? Inason in ɗan fita ganin gari tsorone yake hanani dama." "Zuwa dare kinsan da daddare suke buɗe kantinansu. Khalifa zai zo ya kaimu. Daga nan ma sai ki rakani wajen wata ƙawata" Murmushi nayi mata nace da'ita. Tom Shikenan. Allah ya nuna mana sai in lallaɓa muje nima in gano gari kullum kana ƙunshe a gida" Yawu na haɗiye kana na ɗaura da faɗin . Ni ko Faty Uwani dai bata dawo daga gidan aiki ba tunda muka tafi ko?" Baki ta taɓe tace. "Ki yi tsammaninta dai zuwa shekara guda tim, ko wata shida haka. Kinsan fa su basu fiye son ana zuwa Ijaza ba. Ko mu sanda muke zuwa gidan aiki sai in mun gaji sai muyi ƙaryar ciwo shine zasu barmu mu tawo. Kinsan suna da tsoro gani zasu yi zaki mace musu ma" Dariya muka saka dukkanmu. "Allah kuwa. Haka suke da wannan tsoron. Mu kuma da munji aiki na shirin kashemu, sai mu langwaɓe" Haka mu kai ta taɓa hira. Daga baya kuma duk mu kai bacci, bayan mun yi sallar azahar kenan. Bamu muka tashi baccin ba sai kusan magriba. To ni daman a mugun gajiye nake, ga rashin samun wadataccen hutu. Wanka nayi a gurguje na ɗauro alwala. Faty ta faɗa banɗakin. Ina idar da la'asar ana kiran magriba. Tsakanin magriba zuwa isha a lokacin minti talatinne. Sai da mu ka yi isha Faty ta ajjiye mun wata baƙar abaya tace. "Ki saka wannan a saman kayanki. Ga turare sai ki shafa a jikinki" Karɓan turaren nayi a hannunta. Nayi kamar yadda tace. Ƙarfe taran dare Khalifa ya kirata yana ƙofar gida mu yake jira. Tare muka fito a jere mu uku. Nan naga dare tamkar rana. Kowa a cikin gida da ƙofar gidan sai hada hadarsu suke yi. Masu fita nayi, masu hira da takari nayi, gasu nan dai barkate. Wata baƙar mota me kyau muka shiga. Ina shiga na tarar da wani balarabe me gashi har kafaɗa, ya sa baƙar jallabiya yana ta kallona. Assalamu alaikum. Na furta murya na rawa. Dan naga kallon da yake yi mun yayi yawa. Faty ta juyo ta kalleni ta ɗan kashe mun idanu, ta maida kallonta wajen sima dake kusa dani tayi mishi murmushi. Na fahimci me take nufi sarai, tana nufin kar in ba da ita. Motarmu ta fice a layinmu a guje. " Masmuki ya bint?" Wanda muke gidan baya ya tambayeni da fara'arshi. Ismi Iyabo" Na furta a sanyaye. " Halta kafin? ( Tsoro kike ji)" Ya tambayeni, kafin in yi magana Faty tace. " Hiya daifun min najeriya" Sai ya girgiza kanshi yana mun dariya. " Anti jamilatun jiddan ( kina da kyau sosai) Halnastaɗi'u annakuna sahibain ( zamu iya zama abokai?). Ɗan dariyar yaƙe nayi dan a lokacin bansan me yake nufi da kalmar ba. Sima da murmushin ya bini. Sima kuma sai zungurata yake yi, nayi banza dashi. A bakin ƙaton kanti muka tsaya ko ina lantarki, sai hada_hada akeyi kamar rana. Ni dai ina biye da su Faty zungui_zungui. Wannan abokin saurayi nata ko yaya muka haɗa idanu sai yayi mun murmushi. Ni dai illahirin jikina a mace yake, zuchiyata sai harbawa take yi. Shagon gwala_gwalai muka shiga, abun mamaki saurayin Faty sai sawa yake yi ana cicciro sarƙoƙi manya_manya yana ta karawa a wuyan Faty. Da ƙyar suka ɗauki wata sarƙa da ɗankunne masu kyan gaske. Wannan aboki na saurayin Faty har za a mayar da sarƙoƙin a hallahesu, sai ya sa hannu ya ɗauki wata madaidaiciyar sarƙa mai mannen ɗan kunne, yace da me shagon. " Kam haza?" ( Nawa wannan) Ya tambayi me shagon, ya faɗa mishi kuɗin. Kuɗi ya zaro a aljihunshi ya biya kuɗin sarkar. Aka sa sarƙoƙi biyu a leda daban_daban muka fito. Daga nan sai muka wuce wani gidan cin abinci mai haɗe da ɗakunan kwana. Gurasa ce aka kawo mana da nono da ake dangwalar gurasar dashi, sai shinkafa kaza ( chicken biryani). Ni dai duk a takure nake ainun, ga kallo na masifa. Faty kuwa sai taɓe_taɓensu suke yi ita da saurayin nata, Sima kuwa a teburin wasu matasan larabawa yaje ya zauna abinshi, daga ƙarshe ma suka zame suka barmu daga ni sai Yariman kallo da murmushi ( sunan dana raɗa mishi kenan) "Ma sa'alti nis mi " ( Baki tambayeni sunana ba ƴan mata). Mafi arabiya ( ban iya larabci ba) Na faɗa mishi. "Halnastaɗi'ina antata kallami bil guggati ingiliziyya? ( Kin iya turanci to) Ya tambayeni yana ƙure ni da idanu. Ƙalil_ƙalil ( Kaɗan_kaɗan) "Halnastaɗi'u hannata kallam al'an ( Yanzu zamu iyayin magana)? Na'am ( E) Na faɗa a gajarce. "What bring's you to this country? ( Me ya kawoki wannan ƙasar)? Ya tambayeni tare da bani dukkan nutsuwarshi. I came to work ( Nazo aiki) Na sake amsashi cike da ƙosawar tambayarshi. " Wich tabe of work ( Wanne irin aiki?)" Na yi shiru domin bansan ma me zance mishi ba. Tambayoyin sun mun yawa, daga haɗuwa sai ya titsiyeni da tilin tambayoyi. Ina cikin zancan zuchi sai ga Faty ta ƙaraso tana gyara zaman rigarta. "Yi haƙuri na barki kina jira. Amman nasan Salim uban magana da bin diddigi bazai bar bakin ki ya huta ba. Dan ƙila har kakanki na huɗu ya tambayi sunanshi ko? Dariya ta bani sosai, haka dole na ɗan dara kaɗan. Saurayinta ne ya ƙaraso shima sai gyare_gyare yake yi. Bamu muka koma gida ba sai wajajen biyun dare. Har mun fito a motar Salem ya biyo mu. Ledar wannan sarƙar zinare ya muƙo mun. Tare da gyaɗa mun kai halamar in karɓa. Faty na kalla itama taimun nuni da in karɓa. Hannu nasa na amsa nace. Thank you very much ( Nagode sosai). Sai yai murmushi yace. Halnastaɗi'u annakuna sahibain? (Zamu iya zama abokai) Ya tambayeni. Cike da ƙosawa nace. Na'am" Sai naga yayi wani ɗan ihu tare da damƙe hannayenshi bibbiyu. Ni dai haka na ɗingisa na shige ciki. Faty kuma a wajen na barsu ko me suke taunawa ohon musu. Ɗaki na faɗa ina mayar da numfashi na. Ban wani jima da shigowa ba su Faty suka shigo tana dariya. "Kakarki ta yanke saƙa Iyabo. In dai neman kuɗi kika shigo ƙasarnan da zummar yi. Albishirinki ga mijin Aure sukutum kin samu. Salim yace dani in miƙa soyayyarshi gareki, kuma a yadda ya nuna wallahi sonki yake yi. Kinga kuɗi ya bani yace in baki kiyi siyayya" Kuɗin ta miƙo mun. Wanda a lokacin wannan kuɗi in aka canjasu izuwa kuɗi namu na gida najeriya zai iya kaiwa dubu ɗari. Dubu ɗari me darajar fin million ɗaya a wannan zamanin da kuɗi basu da albarka. To a lokacin kuɗi babbane dubu ɗari, baki na riƙe nace. Ke Faty bazan karɓi waɗannan kuɗin ba ko ba gaskiya ba? Domin bazai samu soyayyataba bazan iya aurenshi ba. Na baro masoyina a ƙasata, ina da yara, iyaye, ƴan uwa. Wannan sarƙar ma cike nake da taraddadin karɓarta. Da ƙyar Faty ta shawo kaina na yarda na amshi kuɗi da sarƙar, dan na miƙa mata nace ta mayar mishi ma ni bana so. "Sarƙar ki saka a wuyanki da'iman kar kiyi wasarere da'ita dan sai a sace. Kuɗi kuma ki adana abinki. Amman wallahi da nice Salim yace yana so da aure, da a mugun guje zan aureshi in watsar da rayuwarnan da nake ciki. Ke kuwa har wanne irin miji kika tanadarma kanki a gida najeriya da kika ƙi amincewa da Salim? Mazan mu sun banbanta da mazan Larabawa, ina miki kwaɗayin shiga cikin babbar daular da har muma zamu dangwali arziki. Akwai Alawiyya data zauna tare dani Balarabe take aure,itama daga Najeriya tazo aikatau, ya ganta tana aiki a gidansu kamar wasa ya aureta yaransu biyu du maza. Duk shekara iyayenta da ƙannenta suna zuwa aikin Hajji, iyayenta sun zama masu arziki. Iyabo ki zauna ki nutsu tsam babu fa wanda yaƙi daɗi" Ni dai nayi jigum inata faman jujjuya maganganun a kaina amman kaina yaƙi ɗauka. Soyayyar Yaya Hamma kawai nake ji tana dukan raina, ina kuma hasaso dimuwar da zai shiga in labarin soyayyata ko aurena da salim ya je kunnuwansu. Wata zuchiyar tace dani. "Ki tsaya kallon ruwa kwaɗo yai miki ƙafa. Kul ki yi nazari dan gudun yin ba wan ba ƙanin. Ki ƙi Salim, ki koma Najeriya batun soyayyarki da Hamma yasha ruwa, ko kiga Daso a gidanshi tunda dama ba furta miki kalmar so yayi ba. Ba wani alƙawari yardadde ku ka yi ba." Sai naji gabana yana dokawa da ƙarfi. Ni dai ji kawai nayi asuba tayi ina daga zaunannan ko kwanciya ban yi ba. Ina yin Sallah saina kwanta bacci. A cikin baccin naji ana ɗaɗamun duka, ina buɗe idanuna muka haɗa idanu da Hajiya. "Maza tashi ki haɗo kayanki, an turo mota zaki koma bakin aikinki." Bani da zaɓi haka na haɗa kayana na fito tsamo_tsamo. A fitowata sai gani ga Uwani kaciɓus. Tayi baƙi idanunta yayi zuru_zuru. Yanayin yadda na ganta a zahirin gaskiya hankali yayi matuƙar tashi. Hannun juna muka kama. Buɗar bakin Uwani maganarta ta farko tace. "Allah yayi zamu gana ne Iyabo. Amman kinga daga nan Najeriya zan koma, inaso in mutu a ƙasata cikin dangina da gatana." Kuka na fashe dashi nace. Uwani ki zauna a wajen Faty ki bani lokaci zan dawo bazaki koma ke kaɗai ba Uwani." "Dalla wuce ni ki bani waje, zaki tsayar dasu kina baiwa" Cewar Hajiya. Ina kuka ina waigen Uwani har gaban motar gidan aikina. Uwani ki mun alƙawarin ba zaki tafi ki barni ba" Ina faɗar haka na shiga mota. Ya ilahi. Azaba, damuwa, ciwon baya dana ƙirji babu irin wanda a ciki ban ɗanɗaneshi ba. Ga tunani Uwani daya addabi ruhina.✍🏻 MRS BUKHARI Su iyabo suna ganin jalala Aimun hakuri yanzu kam na dawo gadan_gadan har saina gama labarin da izinin Allah.🙏🏻 [06/08, 9:35 am] BADI'AT IBRAHIM: *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 ZEE MUSA COLLECTION 💃🏼💃🏼 Tana siyarda atamfofi da laces da shaddar da sauran kayan Yara da shoes and bags da material zee Musa collection ba, anan ta tsaya ba tana siyarda kayan kitchen da supplement da saurankayayakin masu inganci kaidai ka garzaya 🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️Kar ayi Babu Kai ko ka tuntibeta ta wannan number din kamar📞📞08029882667 nagodee 💃🏼💃🏼💃🏼 [8/26, 8:24 AM] +234 803 969 6400: Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 14 MARAƊI Gwadabe: "Amarya ba kya laifi ko kin kashe ɗan masu gida. Ina fatan kin wayi gari cikin aminci?" Ya faɗa mata cikin raɗa_raɗa. Kanta ta sauke zuwa ƙasa kana tace. "Alhamdulillah mijina, da fatan kaima kana cikin ƙoshin lafiyar kamar yadda nake? Murmusawa yayi kaɗan ya jawo hannunta zuwa bakin gado. Daya zauna saiya ɗorata bisa cinyarshi yana wasa da yatsunta. "Hadiza babu abinda zance dake sai dai ince Allah yai miki albarka. Kin kaini wata sabuwar duniya da ban, na gaisheki kuma na yaba da ƙoƙarinki, ya farantamun. Wani daɗine ya lulluɓe Hadiza irin daɗin da ya kasa tsayawa iyakar zuchiyarta. Kallonta yake yi hankali a kwance. A zahirin gaskiya Iyabo ce ke mishi gizo a idanunshi, tare da tunano daren farkonsu, da irin romon soyayyar daya kwasa a jikin Iyabo. Gata mai ƙiba jiki duk laushi da ƙiba. Idanu ya lumshe kawai, haƙiƙa bai taɓa tunanin akwai abinda ka iya rabashi da Iyabo ba face mutuwa. Ashe ƙaddara tuni ta rubuta ƴaƴa ukune kacal a tsakaninsu. Domin kuwa yasan har abada aurenshi da Iyabo ya mutu bazai dawo ba. Tamkar yadda ba'a taɓa mutuwa an dawo ba. "Nace ba. Tunda matar abokinka sun tawo da yara. Me zai hana kawai su zauna ba sai ka sha wahalar zuwa ɗakkosu daga baya ba?" Ajjiyar zuchiya ya sauke kana yace. "Zamu tattauna dasu zuwa anjima inna samu kaina. Yanzu wanka nake so in yi, in fice dan yanzu zaki ga gidan ya kuma ɗinkewa da mata." Miƙewa yayi ya soma shirin wanka. Hadiza ce ta zuba mishi ruwan wankan a bokitin ƙarfe. Kafin ya fito ta ƙarashe gyare_gyarenta. Yana fitowa yace. "Zan shiga cikin gida. Sai zuwa dare zan shigo. Ki shirya zan haɗaki da amaryarki." Fuskarta ya shafa yana murmushi, dan ya hango kishi kwance a idanun. Har ƙofar ɗaki ta rakashi, a madadin ya fita, kamar yadda yace da'ita. Sai ya faɗa ɗakin Amarya. Hadiza tayi murmushi kawai ta komawarta ciki. Tana shirin shiga banɗaki dan ta wanke. Sai ga Balaraba ɗauke da tiren abincin kari. "Amarya uwar gida kuma irin wannan ɗaukar wanka haka" Murmushi Hadiza ta sake. "Ke dai bari Balaraba. Tun ɗazu nake jiran yara ma su shigo su samo mun gaushi a cikin gida, inason yin turaren wuta." Balaraba ta ajjiye tiran hannunta a gefe tace. "Tunda zan sake dawowa kawo ma amaren gidan abinci. Bani kaskon ki yarinya in ciko miki da gaushi" Dariya Hadiza tayi, ta ɗakko kaskonta mai murfi taba Balaraba ta fita. Ita kuma ta faɗa banɗaki ta wanke tas. Kamar an tsikareta ta faɗa kitchen ta soma canja mishi fasali. A kitchen ɗin Balaraba ta sameta ta miƙa mata kaskon cike da gaushi. Kafin kace me Hadiza ta bunke ɗakinta da turaren wutan daya tashi kan amaren gidan, harma da maƙota, wanda su kiya daga Najeriya a hannun Mrs Bukhari gidan ƙamshi. ( Turarene mai tsada na isassun mata. Sau ɗaya zaki turara ɗakin ki dashi amman zai kai sati yana ƙamshi. In kika siya gidanki bai kai sati yana ƙamshi ba. Ni Mrs Bukhari gidan ƙamshi zan dawo miki da kuɗinki) Shafa data jiyo wannan ƙamshi na turaren wuta sai taji ta raina ƙamshin turarukan wutanta da take tunanin zata yaƙi matan Nijar dashi. Damma bata san daga asalin ɗakin da yake fitowarba. Ji kake kawai ana wannan turare ba dai ƙamshi ba. Hadiza tana zaune tana shan farfesun rago sai ga Aminiyarta Luba ta shigo riƙe da hannun ƙaramin yaronta, ɗayan hannu riƙe da ƙatuwar leda shaƙe da kayayyakin ɗa'a inji katsinawa, kayan mata inji Kanawa, maganin mata inji jasawa. "Ashe wannan ƙamshin daga ɗakinnan yake fitowa Hadiza? A gaskiya ban taɓa jin ƙamshin turaren wuta irin wannan ba. Banga laifinki ba yanzu da kika nace ke sai kayan ƙamshin MRS BUKHARI ba. Matar tasan aikinta. Amman dai ƴar maidugurice ko, wannan ƙamshi ya gigitani" Dariya Hadiza tayi ta kamo hannun Luba. "Zauna ƙawata. In dai kayan Mrs Bukhari ne baki ji komai ba, tunda baki shaƙi humrar matan aurenta ba" Zama tayi tana kallon Hadiza. Hannunta da Hadiza ta kama ta shinshina babu shiri ta lumshe idanunta, ƙamshi mai ni'ima ta daki hancinta. "Wannan humra kwai ƙamshi Hadiza" Dariya Hadiza ta kuma sakawa tace. "Kajita, ai humrorinta sunfi da nan. Wannan ƙamshin turaren turara jikine mai riƙe fata kita ƙamshin ƴan kanuri. Luba Mrs Bukhari Kanuri ce, kuma a kayanta babu ha'inci, shi yasa zaki ji kuɗin kayanta ya bambanta gaskiya. Amman muddin kika siya zaki san yaci kuɗinshi. Taso muje ciki in nuna miki humrorinta na jiki, dana gashi ki gani" Ba shiri Luba ta biyo bayan Hadiza, harda sunkuto tiran kayan karin da Hadizan take yi. Gaban mudibi ta kaita. "Kinga wannan humrar matan aurece, ko kishiyarki ba'aso ta shaƙa domin humrace mai sirri" Zaro idanu Luba tayi. "Kaddai kice mun ta asirice, yaushe kika zama haka Hadiza?" Hadiza ta dafa Luba. "Bata asiri bace, ba,a yita da rubutu ba, ba'a yita da wasu surorin Qur'aniba, babu wani surkulle tattare da duk kayanta wallahi sai aiki. Domin ba da ka take haɗa kayayyakinta ba. Sirrin itatuwan mallakar miji sai Kanuri tarihi yasan da hakan. Tasan me zata haɗa da me ya bada kwanciyar hankali. Ƙamshi shi kaɗai rahamane, kuma shi kaɗai zai sa mai gidanki ya yarda dake. Kinga wannan kulaccam ce, wato man ƙamshi me gyara fata tayi laushi tayi ƙamshi. Ko zufa kika yi ƙamshine zai dinga fita. Wannan humrorine masu sirrin ƙamshi kin gansu. Wannan turaren turara ɗakin kwanan Oga ne domin saukar masa da duk gajiyar daya ɗebo a waje, in ya fita kuma yaji bashi da wata nutsuwa data wuce ya ganshi a gidanshi. Waɗannan turarukan wutane iri daban daban, kuma suna da lokutan kunnasu. Ga turaren gashi, ga kulaccam ta gashi, mai sa tsayin gashi, taushi, da ƙamshin gaske. Ga turaren turara gashi, gana turara jiki. Wannan sunanshi gam. Turaren tsugunnone mai maida tsohuwa yarinya. Ga_ga_ga. Hadiza ta dinga jero mata bayani. "Ya isa Hadiza yaushe zaki saka odar wasu kayan ni dai inaso da gaggawa, kuma zaki ɗan samun dan Allah?" "Kwantar da hankalinki zan sammiki. Oda kuma dama akwai kuɗaɗe a hannuna, ki kawo naki saimu tura mata kuɗi ta nita, kayanmu zasu iso cikin aminci. Tana da kostomomi sosai a kasar Nijar sosai, kinsan ƴan Nijar suna son kaya masu kyau da inganci. Tsadar abu in dai mai kyaune baya damun mu" Nan suka zauna zaman cin abinci kuma. "Ga magungunan ki nan, tukuɗinma an daka miki garinshi da dama, saiki dinga samun lafiyayyen Nono kina damawa ki sha. Gasu tsumi kala_kala harda maɗi, akwai na matsi ma. Kinsan lamarin maza sai ka dage barinma ace kana da kishiya kuma budurwa. Sai fa ka dage sosai. A kwana bakwai da zaiyi a ɓarayin Amarya kiyi ƙoƙarin tsuma kanki sosai. Kinga acan ya shiga sabuwar duniyane daban. Kema saiki sabunta baiwar da Allah yai miki. Ita mace tana son sabis lokaci zuwa lokaci inba haka ba, sai kiga injin ɗinta yayi tsatsa, shi kuma tsatsa kashe ƙarfe yake yi duk kyansa, sai ana sabis ana zuba injin oyal." Dariya suka saka dukkansu. A haka dai gidan ya ɗinke da jama'a. Ƙawayen Hadiza na makarantar da take koyarwa suma sai yau suka haɗo kansu suka zo. Kuma suka tawo mata da goma sha taran arziki. "Hadiza ya kamata ki shige gaba muje ki kaimu wajen amaryarki a matsayinki na Babba. Dan na sanki da ɗan banzan kishi. Ya kamata ki watsar da zafin kishi ki bi hanyoyin dabaru na zamani, wanda babu cutarwa, baki da laifi har a wajen Allah " Cewar Madam Chima ƙawa ga Hadiza kuma itace uwar gida a gidanta tana da kishiyoyi har uku. Amman kab cikinsu babu wacce bata sha gabanta ba a wajen miji. Kullum madam Chima mijinta ke goyota a moto ( mashin kenan suke nufi) ya kawota makaranta. Kuma duk abinda yake yi da zaran lokacin tashi yayi zai tawo ya mayar da'ita gida. Hadiza tace. "Ni ai har wayewar garin yau bansan wacce kalace Amaryar ba. Ni ai tunanina ita ya dace tazo ta gaisheni tunda itace ƙarama" Chima tayi shewa tace. "Baki san takan duniya ba. Ai zuwan da zaki yi kankaro mutuncinki zaki yi a wajen mijinku. Ke dai sheƙa kwalliya kisa kaya tsadaddu muje kinji?" Akace mutum baya ƙin ta mutum wai ance da ɓarawo ya ruga. Duk wayonka da dabararka in kaga wani sai kace wannan malaminka ne a komai. Hadiza ta shirya tsab cikin baƙar shadda wacce tasha surfani irinna al'adar ƙasarsu, ta sanya ɗan kunne da sarƙar zinaren da Malam ya basu, ta ɗauko farin takalmi dake cikin akwatin da taima kanta ta saka. Tabi jikinta da humrar Mrs Bukhari, kana tabi kayan jikinta da turaren fesawa na tufafi mai sanyin ƙamshi shima daga Mrs Bukhari ( kina so ƙamshinki ya zam na daban a rasa da kalar turaren fesawan da kike amfani? Ko kuma kyauta kike so na musamman ki baiwa maigida na turare mai sanyaya ruhi kuma kin rasa wanne kikeso? To ina da turaruka na fesawa da nake haɗawa masu sanyi da taushin ƙamshi na mamaki. Hajiya daga yanzu babu ke babu siyan turare Designer babu ke babu zuwa kanti siyan turare. Zan haɗa miki turare naki na karan kanki wanda in kasuwa za'a karaɗe ba za a samu me irin ƙamshin naki ba. Gashi da riƙe tufafi har ki wanke tufafinki bazai bar ƙamshi ba.) Gaba ta wuce ƙawayenta suna biye da'ita a baya har zuwa ɗakin Amarya. Da sallama suka shiga, kafin su ƙarasa shiga falon har ƙamshin Hadiza ya cika falon ya doke turaren wutan da aka turara ɗakin Shafa, dama turaren cikin akwati da ita Shafar ta fesa. Hadiza da Shafa idanuwansu ya sarƙe dana juna. Dukkansu sai suka tsinci kansu cikin damuwa da rashin ƙarfin guiwa cikakke. A fakaice Hadiza cikin sakanni ta karance irin kayan alatun da aka danƙara a ɗakin Shafa. Muryar Ayashe ce ta dawo da Hadiza cikin doka da oda. "Uwargidanmu ga waje ku zauna. Yanzu muke shirin mu kai Amaryar ma ɗakinki sai gashi kin rigamu ma zuwa" Yaƙe Hadiza tayi wanda ya gyara mata fuskarta cikin sakewar murya tace. "Ai babu komai nasan sha'anin biki anata fama da jama'a. Ni ɗinma tun ɗazu naso shigowar." Nan ɗakin ya kacame da gaishe_gaishe a tsakanin dangin Shafa, da ƙawayen Hadiza. A sanyaye Shafa tace. "Yaya ina kwana, ya akaji da jama'a?" Hadiza taji wani abu ya daketa a zuchiyarta yadda taji Shafa na karya harshe wajen lafazi. Bama Gwadabe ba hatta ita salon muryar ta burgeta. "Lafiya lau Amarya ya baƙunta" Wata tsohuwace ta katse maganar ta hanyar cewa da Hadiza. "Dama yanzu zamu kawota wajenki, mu shiga da,ita cikin gidan surukan nata, da manyan gidan. Dan gobe asubar fari zamu kama hanya, anjima kuma zamu leƙa kasuwa muga gari. ( Kunsan ƴan ƙauye akwai son shiga kasuwa ko ba zasu sayi komai ba zasu je suita zare ido) Miƙewa Hadiza tayi tare da yi musu sallama. Shafa tabi Hadiza da idanu ta baya. Dirarriyar mace doguwa son kowa. Kanta ta sauke ƙasa yayin da zuchiyarta taci gaba da harbawa. Ta bangaren Hadiza wannan yanayin ma yafi ƙarfi dam ita sai da ƙwalla ta taru a idanunta. Basu jima da komawa ɗaki ba sai ga sallamar dangin Shafa sun tusota gaba. Tana saye da riga da siket na atampa ɗinkin yan Abuja da wata sarƙa da ɗan kunne fashion me kalar atampar. Mayafinta da takalminta su kuma iri ɗaya amman ko kusa babu kalar a jikin atampar. "To Hadiza ga Amanar Shafa mun danƙa a hannunku ke da Gwadabe. Dan Allah ku zauna lafiya ku rungumi mijinku banda tayar mishi da hankali. In kika ga Shafa tayi wani abun ba daidai ba a matsayinki ta babba wacce ta fita shekaru da hangen nesa sai ki nushetta. Ke kuma Shafa duk abinda zamu faɗa mun riga da mun faɗa miki. Kiyi musu biyayya, kinga a ƙasarnan baki da kowa sai su, duk abinda abokiyar zamanki ta gyara miki ki gyara. Ni da Mahaifiyarki tsawon zaman kishi na shekara hamsin da mu ka yi a tsakanina da'ita girmamawane. Yaya sama, Yaya ƙasa, kuma duk abinda Yaya ta sani shi nake yi. Mu kai zamanmu salamun_salamun dan Allah Shafa kiyi koyi da irin tarbiyyar gidanku" In wannan yayi sai ya cika, wannan sai ya kama. Haka dai sukaita yi. Hadiza tace. "To Allah ya bamu ikon riƙe wannan amana. Allah ya bamu zaman lafiya da fahimta a zaman?" Nan su kai mata sallama kuma. Daga nan su ka kaita ɗakin Yaya Tasi'u shima suka danƙama Anty Badi'a amanar ta musu ido akan zamantakewar. Ita ta rakasu ɗakin matar Jamilu. Sai gatsina take tana magana ciki ciki dai. Daga nan Anty Badi'a ta jagorancesu zuwa dukka ɗakunan amaren gidan, daga nan suka shiga cikin gida shima suka zagaya du ɗakuna huɗun tas. Cikin gidan Malam Anata hada_hadar ɗaura girkin rana. Yayin da baƙin da suka taso daga nesa suketa haramar komawa garuruwansu tunda dai biki ya ƙare. Baba Suwaiba da Amaryar Malam suna dai cikin danginsu anata hada hadane. Amman zuchiyarsu a cike take tab da tsoro da fargabar Malam. Malam ya ɗauki zafi sosai, hatta gaisuwarsu yau Malam yaƙi amsawa abinda bai taɓa yi ba kenan. Kuma ya sake jaddada musu lallai su zauna da zaman shirin dole zasu tafi gidajensu. Kafin ace abinci ya nuna tuni rabi da kwatan baƙin biki ko wacce ta kama gabanta, sai tsirarin ƴan uwa da su kai ragowa su kuma sai zuwa gobe zasu watsr. A ɗakin Baba Suwaiba duk ƴan uwanta sun watse. Amaryar Malam kuma dama mutum ukune suka zo daga ɓangarenta, sai ƙawayenta na maƙota, kasancewar ba ita ke aurarwa ba. Ɗakin Baba Fhatsima ma Altine da Balarabane kaɗai su kai saura, sauran dangi su ana gama karin kumallo ma suka tattare yanasu yanasu suka kama gabansu. Ɗakin Baba Asshine yake cike da jama'a sosai dan su ko soma raguwa ma basuiba. Ƴan takai ma su Laila suna nan, sai su Ayashe, da dangin Amaryar gwadabe, da su Bara'u wanda su kuma gobe zasu kama hanyar suma. DAKIN BABA FHATSIMA:. Balaraba sai faman gyarama Baba Fhatsima ɗaki take yi, ko ina kaca_kaca shine take son ta gyara komai ta ajjiye a mazauninshi. Baba Fhatsima tana zaune sai ta dubi Balaraba tausayinta ya kamata. A ranta saita ƙudurce zata tuntuɓi Tasi'u da batun Balaraba ko Allah zaisa a dace yaji ya amince zai aureta a karo na biyu. Dan Balaraba yarinyace mai hankali sosai, kuma bata da wata makusa da za a ƙita dominta. "Altine gobe Balaraba ba zata biki ba. In zaki tafi ita ki barmun ita. Akwai tunanin da nake yi ne. In hakan ya tabbata zaki ji, amman ki barmun ita gaskiya. Daga Balaraba har Altine wani daɗine ya lulluɓesu dukkansu sun gane inda ita Baba Fhatsiman ta dosa. Kuma shi kanshi Tasi'u ya nuna kamar har gobe yana jin Balaraba a ranshi. "Shikenan Yaya Balaraba ai taki ce kumfi kusa, gata nan" Dariya Baba Fhatsima tayi tace. "Balaraba ai zaki zauna tare dani ko? Duk da babu sa'anninki a gidan. In yaso dan kar kaɗaici ya dameki ba sai ki koma islamiyya ba?" Balaraba tace. "Zan zauna Baba ba komai ai nanma gidanmu ne" Tana gama faɗar haka ta fice ɗakko abin kwashe shara. "Shikenan Yaya Wallahi naso in ɗakkota in kawota wajenki ko wajen Yaya Dije. Acan gabana in banda kuka da damuwa babu abinda take yi. Kinga nan kuma birnice ai nima zanso tayi aurenta a birni. Inta koma islamiyya zata ƙaru sosai. Sai dai bata ɗebo kata da yawa ba" Baba Fhatsima tace. "To in banda abinki ai da kin kawota. Batun kaya kuma Yayansu zai siya mata a ɗiɗɗinka mata ta samu na cin zawarci. Allah dai ya tabbatar mana da Alkhairi. Kije ku duba abincinnan fa ko ya nuna. Kwanciya nake son inyi ko ina ciwo yake yi mun an sha kacaniyar biki. Da kuke_koken yara" Ta bangaren Angwaye kuma, suna ɗakinsu na samartaka suna zubar da zance gami da tsokanar juna. Gwadabe dai Baya cewa uffan sai murmushi, jiya ya ƙara tabbatarwa cewar Iyabo na da wata baiwa da ba ko wacce mace bace zata iya samu ba. Rabuwarshi da Iyabo sai ya sake dawo mishi ɗanye. Har ya gama haɗa ƴan kayanshi da basu shige kala shida, da jakar magungunanshi baice komai ba. Bara'u kuwa ya ƙura mishi idanu yana nazartarshi, tuni ya bugo kuwa jirgin nashi, abotar wasan ƙasa ba abota bace ta wasa. ( Fatima Abdullahi Owuna zanso ace kina karatun littafin Hausa, da a daidai wajennan zaki tuno lokacin muna yara). Hannun Gwadabe Bara'u ya ja zuwa waje, Tamu dama baya ɗakin yana wajen Ayashe suna tattaunawa dangane da maganar barin toye da kahinde da Gwadabe yayi musu. "Gwadabe wai shin duk zuƙa_zuƙan matannan kana nufin basu isa sun maye maka gurbin Iyabo bane? Ya kai da kake da Amare kana tunanin matar da ba mallakin ka ba. Babu mamaki Iyabo tana gidan wannan wan nata Debisi tana aurenta cikin kwanciyar hankali tama rufe shafinka, ta shimfiɗa sabuwar rayuwa. Matar da ko yaranta bata sake waiwaya ba shekara biyu fa." "Sabida kasan naƙi jinin Debisi shine ma dalilinka na danganta Iyabo da aurenshi" Da gaske sai gabaki ɗaya ya hautsine. Bara'u kuwa mai zaiyi ba Dariya ba. Dole shima Gwadaben ya dara, tare da dorawa da faɗin. "Kana ji. Aishi tunanin Iyabo tamkar numfashina yake. Zare tunaninta a gangar jikina daidai yake da zare numfashina. Bara'u Iyabo mutum ce harda ɓari kai shaidane kan hakan, kuma ta cancanci a dauwama ana tunanin ta tare da binta da fatan alkhairi. Fatana shine Allah yasa iyakar ƙarshen wahalar rayuwar Iyabo ya ƙare a gidana. ina mata fatan samun mijin da zai kula da'ita fiye da kima. Kai dai mu ture batun Iyabo mu dawo batun yara. Bara'u." "Dakata malam dallah. Nina faɗa maka gaskiyar abinda yafi dacewa. Ka zauna da matanka a nutse ka gama gane kansu tukunna. Toye saiya gama firamare zai dawo hannunka zancan gaskiya kenan. Zuwa lokacin suma ko wacce da nata. Da yazo saiya faɗa sakandare kai mun wannan alfarmar." Dariya Gwadabe yayi yace. "To Shikenan hakan za ayi duk yadda kuka ce. Shi Tamu yama ƙi yadda zai bani yaran. Naga Toye da Husna sunyi wani irin shaƙuwar data haure misali, ko hakan hujjane. Babu komai in suma sai sun gama firamare ɗin za a bani su duk babu komai" Ana haka sai ga Tamu ya shigo ɓarayin. "Me ake tattaunawa aka wani ja gefe?" Cewar Tamu. Bara'u kuuwa yace. "Maganar Iyabo muke yi daka ganmu" Ƙarasowa yayi kusa dasu yace. "Baiwar Allah. Alkhairan Allah ya kai mata a dukkan inda take. Kai kuma Gwadabe Allah ya baka haƙurin rashinta. In sha Allah nan ba da jimawa ba Toye da Kahinde zasu maye maka gurbin Iyabo a zuchiyarka ta ɓangaren soyayya. Amman Ayashe ta ba da shawarar ka ɗan ƙara haƙuri yaran su sake girma ta yanda za a iya morarsu sai mu dawo dasu. Kafinnan sun samu ƴan uwa ma dayawa su kansu sai sunfi sakewa" Haka dai wunin na yau shima ya mutu murus. Sai zuwa bayan ishane Gwadabe ya samu suka shigo cikin gidan. A ɗakin Hadiza suka ya da zanzo. Ɗakin yasha gyara sai ƙamshin turaren wutan Sandal yake yi. Ita kuma tana kitchen tana ƙoƙarin ƙarashe girkin dare. Kitchen ɗin Gwadabe ya bita bata san yana tsaye yana ƙarema ado da kwalliyarta kallo ba. Ɗagowar da zata yi zata buɗe kula babba danta zubo abincin harda su Bara'u carab sai suka haɗa idanu. A take suka sakarma juna murmushin so, Gwadabe harda lumshe idanu dan wani maganaɗisu ke ɗibarshi. Shi Allahn da yayi shi ya kasance mai son mace mai kwalliya da ado, uwa uba son ƙamshi. Kuma ya lura matan maraɗi ba baya ba wajen iya Ado. "Sai yanzu kuka samu shigowa?" Ta tambayeshi cikin kulawa. Da kulawar shima yace. "Muna kofar gidan tun yamma, gidanne cike dam da mata abinda ya hanamu shigowar kenan. Su Auwala duk tare muka shigo. Ba a kawo abinci daga cikin gida bane naga kina girki?" "An kawo tuwon ɓula su ka yi ne, tunda naga kana da baƙi shine nace bari in dafa shinkafa fara da maka, tunda ina da miya sai ku haɗa. " Abincin ta zuba ta haɗa plate da cokula, ga ruwa a babban jug me kofuna shida. Gwadabe ne ya taimaka mata wajen shigar da kayan abincin..". "Hadiza ki yi mun kiran Shafa tazo mu haɗu aci abincin. In aka kammala sai mu ɗanyi muku nasiha" Jimm Hadiza tayi, ba ta dai ce komai ba, can sai tace.." "Ina ganin kai yafi cancanta kaje ka kirata. Tunda rabonnu da kai tun safe" Bara'u daya cusa nama a baki yace. "Nima abinda zance mishi kenan uwar gida. Kuma ko babu komai akwai iyaye a ɗakin a gaggaisa" Miƙewa Gwadabe yayi ya fice. Hadiza tabi bayanshi da kallo. Ji take yi tamkar zuchiyarta bafa zata iya jure zaman kishi ba. Su Bara'u suna ɗan janta da hira dan hila. Amman taƙi hilatuwa hankalinta na bakin ƙofa taga a yaya zasu shigo. Ga abinci ta zuba ita da Gwadabe ta saka cokula biyu. Shi yana gaba ita kuma tana bayanshi. Saye da materiyal ɗinkin riga da siket wuyan rigar kuma faralas ne. Sai mayafinta da babu ta inda ya dace da shigarta. A ƙasa ta zauna kamar yadda taga Hadiza a ƙasa. Ganin abinci a gaban Hadiza sai Gwadabe shima ya zauna a ƙasa kusa da Hadiza sai ya zamana shi da'ita suna fuskantar Shafa. Mrs Bukhari Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230[8/26, 8:24 AM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 15 "Yaya Bara'u ina wuninku? Yaya barka da dare ya akaji da taro?" Sai lokacin Hadiza ta fahimci ashe lalacewa tayi wajen kallon Shafa, yanda take wani gwalangwaso kamar babu ƙashi a jikinta. Sai da ta sauke ajjiyar zuchiya kafin tace. "Taro alhamdulillah, ya baƙunta,?" Murmushi tayi gajere kawai. Shi kuma gogan sai yace. "Matso ga abinci muci tare. Hadiza bata cokali" Dole ƙanwar naƙi kenan. Haka Hadiza ta ɗakko cokalin ta miƙa ma Shafa. Sai jujjuya shinkafar take yi ta kasa kai ko loma bakinta. Shafa da Gwadabe kuwa bil haƙƙi suke cin abincinsu. Carab a idanun Hadiza suka sakarma da juna wani murmushin ƙauna wanda ya kusan tarwatsa kan Hadiza. Shigowar Auwala da Amaryarshi Shatu, da Mammada da Amaryarshi Nana ne ya sanya Hadiza ta ɗago da fara,'arta ta tarbesu. Matan a ƙasa suka zauna, Mammada da Auwala kuma suka zauna a sama. "Amare kun sha ƙamshi, kun rigamu shigowa naso in shiga da yamma to na ɗan tsaya yin gyare gyarene. Bari a zubo abinci ko?" Auwala da yasa hannu a abincinsu Bara'u ya soma ci yace. "Yauwa dama Shatu taƙi cin tuwon ɓula wai ita shinkafa zata ci. Dama naso daga nan in kaita ɗakin Anty Badi'a ne nasan zamu samu abinci. Mammada zo mu muci nan. Hadiza ƙaro mana" Ya miƙa ma hadiza tiran abincin ta zuba musu. Nan ta zuba ma Amaren Yayun nata. Gwadabe da Shafa sai abincinsu suke ci, anata nishaɗi. Su Shatu ma suka saki jikinsu suka ci abinci. Hadiza fa sam taƙi cin abincin da wayo_da wayo. Bayan duk an kammala cin abincin sai su Bara'u suka haɗe nasihar da zasu yi musu du harda matan su Auwala. Daga haka kuma suka yi ma Hadiza Sallama, tare suka fita dasu Auwala da matansu zasu kaisu ɗakin Yaya Tasi'u da Yaya Jamilu. Ɗakin ya rage daga Gwadabe sai matanshi. Tattare kwanuka Hadiza ta soma yi. "Zauna Hadiza inaso in ɗan yi magana daku nima" A sanyaye ta ajjiye kwanukan ta zauna a ƙasa shi kuma yana bisa kujera. "Da farko dai ina mai roƙonku arziki ku haɗe kai ku samar da farin ciki, nutsuwa, zuriya ta gari a gidannan. Dole ku haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen haɗe kawunanku. Kar ku bari wasu su shiga rayuwarku su yi ƙoƙarin tarwatsaku. Gidannan cike yake da facaloli ke Hadiza kinsan komai. Nima ina da ilimi akan irin zaman, ni da Iyabo mun zauna tare da su Yaya Hambali, babu irin gulme_gulmen da ba'ayi a tsakankanin mata. Ni bazan hanaku tsaɓin kawaye a cikinsu ba, amman na horeku da ku iya bakunanku. Duk da dai ku ba mazauna bane, ke kina aikinki na koyarwa itama Shafa Yaya Tasi'u ma yace ta bashi takaddunta zuwa gobe in aka nutsa zan kai mishi zai samar mata aiki. Dan Allah ku taimaki talakan mijinku ku bashi nutsuwa, aikina na wahalar gaske ce ina roƙonku da ku samar da farin ciki a gidannan. Ni in so samune yau in ganku a wannan ɗakin gobe in ganku a ɗakin Shafa kuna hira kuna dariya." Fasali yaja tare da ɗan yin murmushi, suma murmushin suka mayar mishi. "To kasancewar gobe zan bar ɗakin uwargida, kamar yadda addini ya tanadarma matar data taɓa aure inta kuma wani aure kuma tana da kishiya kwana uku Shari'a ta tanadar mata. Hadiza a matsayinki na babba da kwanan da rabon girkin na baki wuƙa da naman faɗin yadda za'ayi, kuma in sha Allah yadda kika ce hakan za'ayi" Hadiza wacce ƙwalla ta taru a idanunta tun lokacin da Gwadabe ya kirata bazawarar data taɓa aure a gaban kishiyarta, kuma ta ɗauki hakan a matsayin tozarci. Ta ɗanyi yaƙe tace. "Nagode da wannan girma daka bani. A babin maslaha ina ganin tunda du mu biyun masu fita aikine zaifi kyau ace ko wacce ta dinga girkinta kawai, gudun shiga hakkin wani. Dangane da rabon kwana kuma ayi kwana uku_uku. Sannan ni na baka damar shiga ɗakin Amarya a darennan kwanana guda ɗaya na yafe shi naci girma." Tsam Gwadabe yayi yana karantar yanayinta da duk ya sauya, ya riga yasan da Hadiza zai samu matsala kishinta yayi yawa. Yanata tunanin to meye abunda ya ɓata ranta yanzu_yanzu. Kawar da tunanin yayi da cewa. "Ba za'ayi haka ba, kuma ai akwai danginta a ɗakin sai zuwa gobe zasu kama hanya. Dangane da rabon girki da kwana naji abinda kika ce, kuma dama nayi miki alƙawarin duk yadda kikace ta zauna. Inaga in kuna da wani ƙarin bayani zaku iyayi" Du su biyun suka ce basu da wani ƙarin bayani. Sallamar Shafa yayi ta koma ɗakinta. Hadiza kuma rai a murtuke take ta faman kai kawo na fitar da kwanukan da aka gama cin abinci. Ruwan wanka ta kai mishi harda ɗiga mishi wannan haɗaɗɗen turaren wankan data siya a hannun mai gayya mai aiki Mrs Bukhari ( kema ki mallaki naki yana da sirri) "Na kai maka ruwan wanka kaje ka watsa" A madadin ya tashi sai ma ya riƙo hannunta yai mata masauki a cinyoyinshi, dan nauyi sai da ƙashin guiwarshi yayi motsi mai zafi. Shi ya ƙura mata idanu, ita kuma ta ƙurama ledar tsakar ɗakinta idanu. Can sai hawaye shar_shar suka soma zubo mata. "Ya Allah Hadiza menene ya kawo kuka kuma, shin nayi wata maganar data sosa miki ranki ne?" Shiru tayi shima shiru yayi yana kallonta da dai yaga abun bana ƙare bane sai ya rungume abarshi yaima bakinta riƙon alawar yara. Ji kake shiru sai sautin ajjiyar zuchiyar Hadiza. Sun jima a cikin wannan koramar da kyar ya zare jikinshi a nata. Miƙewa tayi da sauri, yai mata dariya tare da girgiza kai. "Ke ba yarinya ba, amman kinfi yarinya shagwaɓa bari in fito wanka sai kin faɗamun sanadin zub da hawayennan kina Amarya" Dariya tayi kawai. Shi ya wuce wanka ita kuma ta wanke kwanukan da akaci abincin a ƙaton bawo a kusa da kitchen ɗinta. Tana ganin shige da ficen Dangin Shafa. Yaya Tasi'u ne yazo wucewa. "Yaya Tasi'u sannu da dawowa" kallonta yayi yana dariya. Hannayenshi rike da ledoji kawai saiya miƙo mata leda ɗaya. "Zo ki karɓa Hadiza rabonku ne dan tunda na shigo gidan banci karo da kowa ba" Da sauri taje ta amshi ledar tana murna tare da yi mishi godiya. "Ina Gwadaben?" "Wanka yake yi, ni kuma wanke_wanke na gama" Kafin ya bata amsa Yaya Jamilu ya shigo gidan shima. Abun mamaki wucesu yayi ba tare da yayi musu sallama ba balle ya tsaya a gaisa, ɗauke kanshi yayi kamar ma bai gansu tsaye ba. Tasi'u ya girgiza kai yace. "Allah ya nuna mana lokacin da iyalan Malam zasu haɗe kawunansu su mayar da damuwar ƴan uwansu damuwarsu. Sai da Baba ta faɗa dama haɗakaarnan babu abinda zata haifar face sabon rikici. Jafaru da matarshi ne suka fito daga ɗakin Zangina, sai fa da suka zo dab damu Jafarun yace. "Sannunku" Itako matar tashi kalloma basu isheta ba" Kasa amsawa dukkansu suka yi suka bisu da idanu har saida suka shige ciki. "Jeki ciki Hadiza kinji. Allah ya bamu lafiya sai da safe" Jiki a mace Hadiza ta shige ciki. Lemo da ayaba ne a cikin ledar da Yaya Tasi'u ya bata. Lemun ta yanka musu ta saka a plate, Gwadabe na shigowa falon ƙamshin turaren wankan data zuba mai ya daki hancinta. "Ina kuma muka samu lemo?" Yai mata tambayar yana mai ƙureta da ido. "Yaya Tasi'u ne ya bani. Haɗuwa muka yi shi zai shige ɓarayinsu, yace a gaisheka" "Ayya ina amsawa." Wanka Hadiza tayo itama, a daren Gwadabe ya mantar da'ita wata damuwa data ɗaurama kanta. Washe gari kuma Dangin Shafa Amarya da su Goggo Iyatu duk suka ɗunguma suka kama hanyar Takai, su Goggo Iyatu ko sallama ba sui da Gwadabe ba balle Amaren shi. Sai su Sakina da Ayashe ne kawai suka shigo su kai sallama da Hadiza. Gidan ya gare daga sabbin Amaren sai su Yaya Tasi'u. Tun bayan tafiyar ƴan Takai Shafa ta shiga aikin gyaran ɓarayinta, daga cikin uwar ɗaki zuwa falo, zuwa kitchen. Daga cikin gida yauma aka kawo musu abincin karin kumallo. Tun bayan data ga Gwadabe yayi ma su Bara'u rakiya zuwa tasha, bata sake sanyashi a idanunta ba har azahar. Tana zaune tana cin nakiya tana kurɓar shayi sai gashi ya shigo da fara'a ɗauke a fuskarshi. "Amarya bakya laifi daɗi ake ci ne?" Murmushi tayi mishi kafin tace. "Kaga nakiya ce nake ci na ɗan soma jin yinwa" Zama yayi a kusa daf da'ita ya gutsiri nakiyar ya jefa a bakinshi. Yana ƙarema ɗakin kallo yanda ta sake mai fasali yafi na farko fiye. "Me yasa baki ɓararraka ko taliya bace, ba naga taliyar Hausa a kitchen kusan kwalla uku ba, ai ko mai da yaji sai ki zuba. Tunda su Baba Fhatsima sunma yi ƙoƙari suma suna buƙatar hutu. Naji gidan duk ya kaure da ƙamshi da halama amaren gidan sun soma girki" Sailuba ɗiyar Yaya Tasi'u ce tayo sallama ta shigo. Hannunta riƙe da filas ɗin abinci, a gabansu ta dire tare da gaishesu cikin girmamawa. "Innata ce tace in kawo. Tace kiyi haƙuri aikine yai mata yawa sai yanzu ta sauke sanwar" Murmushi Shafa tayi tace. "Babu komai kice mata nagode Allah ya saka da Alkhairi" Da "Ameen" Sailuba ta amsa tai musu sallama ta fice.Shafa kuma tayi sauri ta ɗakko plate da cokula biyu ta juye musu abincin. "Bismillah mu ci ko tunda dai kana nan aka shigo da abincin " Bai mata musu ba sai yayi kamar yadda tace dashi. Hadiza kuma tana can ta tusa abinci a gaba tana jiran shigowar Gwadabe su ci, yace zai ɗan leƙa Shafa a tsaitsaye. Yau zai shigo, gobe xai shigo, saida ya share awa uku kyawawa. A wannan lokacin Hadiza ta kai maƙura wajen ɓacin rai. Abincinta ta zuba tayi shigewarta ɗaki ta zauna kenan akan gado ta jiyo yana sallama a falo. Jin motsin cokali a uwar ɗakine yasa ya leƙo uwar ɗakin suka haɗa idanu, take yasha jinin jikinshi, amman lokacin sallah ya riga da yayi haka dole yayi alwala ya tafi masallaci. Yana dawowa kuma kamata yayi ya ɗebi ƴan suturu ko kala ukune ya koma ɗakin Shafa daga la'asar kwananta zai soma. Har ya gama ɗiban kayan da zaiyi amfani dashi Hadiza tana daga kwance tana kallonshi, sai tubka da warwara take yi. Wani irin muƙu_,muƙun kishi ke turniƙeta. A kusa da kanta dab ya zauna yana shafar sumar kanta dake sheƙi da ƙamshi. "To ni kam zan tafi Hadiza. Sai bayan kwana bakwai zan dawo. Zanyi kewarki sosai, tare da wannan ƙamshin naki mai tasiri a zuchiya" Wani kallo tayi mai shi ba harara ba, shi ba kallon so ba. Dan ya kasa fassara irin kallon.. "Abincinka dake ajjiye a falo fa, kaci ne?" "A'a ɗazu ina shiga ɗakin Shafa Sailuba na kawo abinci. To shine shafar ta zuba mana, kinga ai ba zata ji daɗi ba in banci ba, kafin zuwan Sailuba kuma naci nakiya" "Agen? Hmmm shikenan a sauka lafiya ango. Lallai ga zumuɗin yage tantani nan ina gani a tattare da kai. Nutsuwarka harta gushe sabida kula da kai zai koma hannun Shafa " Baki ya buɗe zai yi rarrashi. Tayi saurin ɗaga mishi hannu, sai kuma ta fashe da kuka. Ƙur yayi yana kallonta kawai yana tunanin irin danƙareren aikin dake gabanshi. Dan ya lura Hadiza bats son a zauna lafiya balle a samu haɗin kan da zai samar da nagartattun ƴaƴa. Da wuri ya kamata yaima tubkar hanci dan gudu kada wankin hula ya kaishi ga dare. Masu iya zance na cewa. Itace tun yana ɗanye ake tankwarashi, matsawar ya bushe to sai dai a ɓallashi. Dannewa yayi ya shiga aikin rarrashinta da shafar bayanta har tayi shiru. Tana gani ya fice a ɗakin Izuwa ɗakin Shafa. Tohfa MRS BUKHARI 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 [8/27, 12:51 PM] +234 803 635 0240: NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 16 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 IYABO:. Lalubo lambar Yaya Hamma nayi a wayar Faty na danna kira. Nan take zuchiyata ta shiga harbawa fafafat, ina jiyo motsin sonshi a zuchiyata. ( M Farida Ana magana )Sau uku ina gwadawa number bata ma shiga, kamar ma layin a ƙasa yake baya cikin waya. haka dole na haƙura, na bari zuwa wayewar gari, in sake jarabawa ko Allah zaisa in dace. Bacci a ranar lafiyayye muka samu mai nutsuwa. Bayan munyi sallar asuba ma bacci muka sake komawa ba mu muka tashi daga baccinnan ba sai azahar, ni dai akwai gajiya marar adadi tattare dani, haka ma Uwani. Faty kuma dama ita ɗabi'ar baccinta kenan. Alwala muka ɗauro bayan duk munyi wanka. Kayan jikinmu muka mayar dan kayanmu na cikin mots ba'a sakko dashi ba. Ina sallah Salim ya shigo, abinci ya kawo mana da burosai na goge baki da makilin. Kafin in idar ya fice. Ina idarwa ya sake shigowa da wata zungureriyar leda shaƙe da dogayen riguna da takalma harda agogo, da tarkacen kayan kwalliyan mata harda turare. Ya miƙo mini, nasa hannu na karɓa ina mai mishi godiya. Sai cewa yayi dani da harshen larabci. "Ki shirya zan gabatar dake a wajen dangina. Kakata ma tana nan sai su ganki" Na dubeshi, sai yayi mun murmushi. "Tuni labarinki duk ya karaɗe familyna. Na faɗa miki sonki nake yi da aure ba da shashsnci ba. Tun rabuwar dake zuchiyata bata huta ba wajen begenki da mafarkin mallakarki" Ya sake faɗa. sai na gyaɗa kaina nace mishi. I am coming ( ina zuwa) shiga uwar ɗaki nayi na tarar da Faty tana waya. Uwani a falo na barota. Faty wai ashe da gaske salim yake yi aurena yake so yayi? Kinga fa kaya ya bani wai in saka mu sauka ƙasa zamu gaisa da iyayenshi. Sai ta zare wayar a kunnenta tace. "Kwarai kuwa. Komai a rayuwa yana da sanadinshi. Da kina Najeriya babu dalilin da zaisa ku haɗu da Salim har ya soki, tunda baisan hanyar Najeriya ba." Faty akwai Matsala ne akwai ɗan uwana da mu kai alƙawai dashi kafin in baro ƙasata" Buɗar bakin Uwani wacce shigowarta kenan sai tace. "Akwai dai wanda kika ɗafa sonshi a ranki dai banza. Yanzu haka yama mance dake. Babu mamaki in mutumin ƙauyene kije ki iskeshi da mata huɗu ma, kinga babu wajen zamanki a gidanshi ai. Yanzu kamar wannan bawan Allah yaji sonki kina neman kisa ƙafa kiyi fatali da damarki. Wai Iyabo a ƙauyen ƙayayau ɗinnan kike so kiyi rayuwa, kina ɗaukar tallar nono aka? Ke sha'awar rayuwar kenan kike yi. Koko sabida fari, gashi da tsawon Hamma ke ruɗarki? Duk da dai nasan ba hakan bane tunda Salim ya kere Hamma a komai. Amman dai Iyabo Allah ya wadaran wannan zuchiyar taki ta gaban ƙirjinki" Ta ƙarashe zancan ta tana hararata Turus nayi ina kallo da sauraren Uwani da take ta balbalin faɗa kamar Uwata. Faty ce ta katse hirar da cewa. "Yanzu dai ki shirya kije ki dawo mayi magana. Uwani mu karya kafin ta dawo" Ni dai a tsorace du nake. Doguwar baƙar riga na saka mai shegen kyau, da takalmina baƙi mai tsini, na yane kaina da mayafin rigar tare da feshe jikina da wani turare mai ruwa ja. A tsaye a inda na barshi na sameshi. Ba sai mutuminku ya nemi lalacewa dan kallona ba. Ni kuma sai kunya ta kamani a raina sai nake ayyana. Wannan kallo da yake yi mun kallon yaudarace kawai, su da suke da haske da kyau, matansu Allah ya basu diri da cikar ƙirji. To ni meye a jikina na kallo da har za'a shagala in ba ɓaka_ɓakan mazaunai ba? Ashe shi yasan dalilin, tare da larabawa masu auren ɓaƙaƙen fata, da turawa masu auren baƙaƙe su bar kyawawan fararen matansu. Haka muka gangara a jere muka tadda ahalin gidan a daining table babba suna cin abinci. Da ganina wata tsohuwa ta iso inda muke ta riƙo hannuna har gaban daining ɗin. Zaunar dani tayi a kujerar kusa da wani tsoho. Shima Salim ya samu waje ya zauna. Jikina yana ɓari na gaishesu da larabcina irin nami na ƴan koyo. Da soyayya gami da fara a suka amsa mun. Ya dinga nuna mun ƴan uwanshi, yayye da ƙannenshi. Ga mahaifiyarshi da mahaifinshi, sai kakarshi da mijinta, sai kuma Yarshi Sarla da mijinta Umaid. Ni dai duk ina zaune a mugun takure, su kuma sai jana da hira suke yi. Mahaifiyarshi ta tambayeni asalina. Ban ɓoye mata komai ba kama daga yarena, izuwa aure da nayi a baya da adadin yarana. Duk da haka sun yi na'am dani. Abu guda dana fahimta da larabawa ko basason abu. Muddin yaransu ya nuna Yana so, to suma zasu koyi son wannan abun. Suna da son yara, su kuma yaran sai suke Amfani da hakan wajen tursasama iyayen son ra'ayinsu da yarda dashi. Gurasa da nono aka zuba mun sai shayi, a kunyace na ɗan cakala Salim yace in tashi ya mayar dani. Sai mahaifiyarshi tace ba za'a yi haka ba. Ya ɗaukemu daga ɗakinshi ya dawo damu wani ɗaki dake kusa da nata, ɗakin ƙanwarshi dake karatu a landan. Haka kuwa akayi, ɗakin yafi nashi kyau da kuma yalwa. "Ku shirya zuwa dare sai mu fita daku kuyi siyayya, ku ga gari kuma." Cewar Salim bayan mun samu keɓewa nake sanar mishi ni Najeriya muke son komawa, zaman bautar da muke yi ya ishemu. Anan yai mana alƙawarin zaiyi mana cuku_cukun visar da zamu koma, zaima biya mana, amman in mishi alƙawarin zan bashi damar kafa soyayyarshi a zuchiyata dan shi da gaske aurena yake son yi. Tuni na amince mishi da hakan magana ta domin Allah ba har cikin zuchiyata ba amma. Da daddare ya fita damu zuwa wani super maket babban gaske na suturu masu tsada da masu arha duk gasu nan. Mu ka dai tsittsinci abinda ba a rasa ba haka. Ya biya komai muka sake nausawa zuwa zagayen cikin gari. Ni dai banyi ƙumun baki ba nace mishi ni kam inason yin Umara. Ranar juma'a yai alƙawarin zai kaimu da izinin Allah. Ai kuwa hakan akayi. Daga umara muka shiga kasuwar DOGON GIDA dake Makka. Anan muka ga dandazon maza da mata na Najeriya iri iri. Ga gumama a zube a ƙasa, ga sababbi, zannuwan gadone, takalma. Komai da komai dai. Nan Faty ta dinga kutsawa damu. Siyan kaya muka dingayi. Ni da Uwani mune harda maƙala haƙori makka bibiyu a bakunanmu. Adai taƙaice mun kaso kuɗi masu yawa, daga haka muka koma Jidda, nanma suna da babbar kasuwa Faty ta kaimu, ni har dilar zanin gado, da kayan mata dogayen riguna da takalma na siya za a ɗauro mun a jirgin kaya. Ɓangaren kayan kitchen hatta plate da cokali saida na siya, na sai manyan kuloli kala biyu, masu filas na shayi. Uwani kuma dila biyu na zannuwan gado da dilar Kayan sawan yara ta siya. Daddumai, da carbi, bagaruwa, dabino, ruwan zamzam kuwa sunfi komai yawa a tsarabarmu. Naima Dada tata tsarabar, naima Iyaa Debisi nata daban, naima Yaya Hamma nashi daban shima. Su Boɗɗo kuma saina isa Najeriya zansan mai Zan cire musu dai, ragowar kuɗaɗen muka canjasu zuwa kuɗinmu na Najeriya.. Duk wannan siye_siyen da taimakon Salim, da taimakon mahaifiyarshi danta bani kuɗi a gaskiya masu kauri. Suna da wani irin karamcin da a ɗan kwanakinmu a gidan Salim harya soma samun gurbin zama a zuchiyata. Kwananmu takwas a gidansu Salim Allah ya kawo lokacin dawowarmu Najeriya, mahaifiyarshi da danginshi su kai mana goma sha tara na arziki, har zoben gwal yarshi Sarla ta bani ɗan ƙarami na maƙalashi a hannuna. Duk tarin kayayyakinmu mun ɗaure zasu tawo a jirgin kaya wanda akace bazai wuce wata ɗaya ba zai iso. Sai ƴan akwati da jakunnanan kaya, da jakar hannu kawai muka riƙe. Har filin jirgi Faty ta rakamu, Salim shima yana wajen tare da Yarshi. Sai sake jaddadamun yake yi akan in riƙe mishi alƙawari, sannan zai biyo adireshin gidanmu na Kano dana bashi yazo a kawoshi har ƙauyanmu nanda sati biyu in ya rage abubbuwan dake gabanshi. Sarla itama sai sake roƙona take yi akan kar in yaudaran mata ɗan uwanta. Zai zo da kanshi neman aurena. Ni dai duk sai jikina yayi sanyi tuɓis, har na soma kokonton wanda zan ɗauka da wanda zan ajjiye. ( To masu karatu wannan zaɓi ayi daku. Ku wa kuke ganin ya cancanta Iyabo ta ɗauka Hamma ko Salim?) "To Faty Allah ya sada fuskokinmu da Alkhairi. Zamu dinga waya in sha Allah. Da haka mu kai sallama da juna. Muna hawayen farin cikin komawarmu ƙasarmu Najeriya. Faty tana kukan sabo, Salim da Sarla suna cikin alhini da fargabar kar in yaudaresu. Da misalin ƙarfe Taran safiyar ranar laraba jirginmu ya tashi daga king Abdulaziz Airport jidda. Tafiyar awa biyar da minti hamsin da biyar ce ta sauke mu a Airport na Legos Murtala Muhammad. Kai tsaye daga Airport muka wuce tasha. Wata sassanyar iskar ƴanci na kaɗamu zuchiyoyinmu cike da farin ciki marar adadin kwatance. Tiket muka siya, motarmu sai ƙarfe biyar na yamma zata tashi tafiyar ta dare ce. Masallaci muka samu mu kai Sallah. Uwani muje mu nemi abinci mu ci yinwa kamar zata kasheni" Na faɗa ina riƙe cikina. Wani ɗan ƙaramin gidan cin abinci muka shiga. Abinda suke siyarwa tuwon eba da miyar ganye, sai sakwara da miyar egusi. Sakwarar muka siya da nama gunduna_gunduma. Muka ci mu kai ƙat, kana muka koma masallaci, mun bar motar da zamu shiga anata lodin kaya. Bayan la'asar muka shisshiga mota kowa ya zauna a muhallin zamanshi. Gaga_gaga sai gamu a Kano ta dabo tumbin giwa ko da me kazo an fika da misalin ƙarfe shiddan Asuba, garin da duhunshi a lokacin. A tasha muka sallaci asuba. Uwani gidanki kika nufa ko gidan Hajiya?" "Gidan Hajiya dai zanje, in yaso shi Hafizun yazo ya sameni a gidan, zan aika Habu ya nemoshi" Mota muka shiga har zuwa bakin layinmu. Muna sauka sai gamu ga Lekan da abokinshi suna atisaye. A guje Lekan ya karaso. "Ahh Antimi Iyabo. Okaabo" Farin cikine ya lulluɓeni marar adadi. Jakunkunanmu suka kinkima, abokin Lekan yabi Uwani, ni kuma Lekan ya bini. A kofar gida muka samu Iyaa Debisi tana shara, ga shago harta buɗe. Ɗagowar da zata yi muka haɗa idanu. Saina fashe da kukan farin ciki dan ada na fitar da ran sake sanyasu ga idanuna. Iyaa ai saita soma wannan kwakwazo data saba, kafin kwabo jama'ar gidanmu duk suka firfito ciki harda yemisi da titsetsen cikinta a gaba, ko me take yi a gida duku_duku ohon mata dai. Iyaa Kokodeen ce ta ja hannuna zuwa cikin gida ɗakin Iyaa. Nan aka shiga gaisawa da tambayar bayan rabuwa. Sai cewa suke yi nayi kyau na yi haske, amman na rame. Ni dai sai dariyar yaƙe. Ruwan wanka Lekan ya kaimun, na shiga na gargasa jikina. Kafin in fito nazo na tarar da kwanukan abinci har daga maƙota. Sannan matan unguwa har sun soma cika gidan anzo yimun sannu da zuwa. Na zama kamar watan ramadan, kowa sha'awata yake yi haƙorina na maka har biyu maƙale a bakina sunata sheƙi, na fahimci hakan ya ƙaramun kwarjini sosai. Ni dai sai yaƙe baki nake yi, amman ta ciki na ciki. Amala naci na ƙoshi na sha baƙin bunu. Kwanciya nayi dan in ɗan huta, dan a niyyata gobe in Allah ya nuna mana zan kama hanyar ƙauyanmu, suma in gansu su ganni, sannan inga ajiyata dana ajjiye.( Maƙiyan Hamma ya jiki? 🤣) Bani na farka ba sai azahar, Burodami Debisi da Burodi Kokodeen suna ɗakin, ga yemisi a gefe ana musu sulhun da aka saba. Burodi Debisi muna haɗa idanu yayi mun murmushin da ada in banyi mafarkin irinshi daga gareshi ba yau, nayi gobe dan tsananin yadda nake mafarkin in zama matarshi. Sai gashi kash yanzu idanunshi a kulle suke akan sona. Yayinda nima idanuna suka makance akan son Yaya Hamma. "Iyabo kece kika sake wani kyau da kwarjini haka? Kai maraba lale da shigowa ƙasarmu me albarka." Kaina na sunkuyar dan bazan iya juran irin muguwar hararar da yemisi ke watso mun ba. Kafin in gaishesu Yemisi tace. "Dama a wannan karon ke kike barazanar kashe mun aurena sai gashi kuma kin dawo gida. Dan Allah in aurenshi kikeso kiyi me yasa tun farko ba kui aurenba, me yasa zaki ɗauke tunanin mijina daga gareni" " Mama Iyare Yemisi ( Kinci uwaki Yemisi)" Iyaa ta zageta, dama dai jira take yi sai ta sau kuka kawai. Ni kuma so nake in yaɓa mata maganar da zata sake ingizata amman saina gaishe da Burodami Debisi, da Burodami Kokodeen, Kokodeen yace. "Tunda kika tafi ba'a waya dake. Iyaa har ramewa tayi sabida tunanin ko kina lafiya. Hakama Dada da wani dogon ɗan uwanku Hamma. Dan duk sanda Dada zata zo tare suke zuwa, suna yawan zuwa in banda kwana biyunnan da basu zo ba muke tunanin ko ba lafiya ba.. Gabana ya yanke ya faɗi ras jin an ambaci ba lafiya ba. Yanayin aikine, kuma ni bama waya a hannuna shiyasa. Gobe sassafe nake so dama in wuce Jeren." Burodami Debisi yace. "Ki zauna ki huta mana kafin ki tafi" Iyaa tace. "Gara taje, ina tunanin Daso ko babu lafiya fa. Wannan karon sun jima basu shigo ba . Gobe ta kama hanya kawai. Ki yi sallah sai mu tattaka mu je gidansu Uwani kafin Hajiyarta ta rigamu zuwa aji kunya" To Iyaa" Ina faɗar haka na miƙe na fice ɗauke da buroshi da makilin dake jakata. Bakina na goge na ɗauro alwala na shigo. Dabino da bagaruwa da na jefo a jaka da ruwan zamzam na ƙananun fararen roba na ciro ƙullin nasu Iyaa na ajjiye mata. Ga wannan Iyaa, kayanmu suna jirgin kaya. Ba zasu wuce wata guda ba, dan munyi sare_sare sosai ne" Nan Iyaa ta soma rawa tana shi mun albarka. Ai kuwa wannan dabino sai Iyaa ta shiga aikin kididdibashi ana kasabta harda maƙota ma. Da haka suka ci gaba da shari'ar Yemisi dake gabansu, Iyaa ta lallaɓata tasa Debisi ya bata kuɗin cefane akan da yamma zata koma. Ina Idar da Sallah na saka doguwar jallabiya irin baƙin larabawannan ni da Iyaa muka kama hanyar gidansu Uwani. A hanya ne take sanar mini cewar sunje dubo Yarana dai aka tabbatar musu wai yaran suna Abuja wajen Matar abokin Gwadaben. Ajjiyar zuchiya na sauke nasan ko babu komai zasu samu ilimi. Allah shine masani idaniyata cike take da son ganin Ƴaƴana. Amman nasan ƙila yarannan sai sun girma a kwatanta musu inda nake rayuwa su neme ni. Ina musu fatan samun nasara da dacewa akan dukkan abinda aka ɗaurasu akai. Inma karatu, inma sana'a domin dogaro da kai. Daga su hai mahaifin nasu ina musu adda'ar samun ɗaukaka. Har a ka'aba na yi musu wannan adda'ar na jaddada. Da tulin tunani da misalai muka shiga gidansu Uwani dake cike. Ƙannenta duk sun cika gidan, da yaran kawunta dake aure da yaransu. "Ahh Toyosi yau kune a tafe. Sai kika ga baƙin larabawa sun sauka" Cewar Hajiyan Uwani. Musa wanta yana zaune yana cin bagaruwa Yace. "Kaga Hajiyoyin ƙannenmu Makka kiran Allah, kun sha aikin Hajji da umara har kun gaji, ga sallar juma'a a masallacin ma'aiki arrasul S A W." Na kalli Uwani dake daga cikin ɗaki Hafizu da yaranta suna maƙale da'ita. Ido ta kashe mun, ni kuma nayi dariyar da mu kaɗai muka san fassararta. Ai kuwa Musa ya saki ihu. "Ihuhu jibi haƙorin makka yadda yake ƙyalli a bakunanku. Dan Allah ko umara ku biya mana da ramadana dai mu je" Ni dai sai Dariya nake yi. Hajiya na gaisar na shige ɗakin da Uwani take. Iyaa kuma suka shige ɗakin Hajiya. "Iyabo barkanku da dawowa baƙin larabawa" Zama nayi yaran duk suka rufeni. Safwan na ɗauka ya girma sosai. Hafizu ina yini mun sameku lafiya?" "Lafiya lau sai alkhairi. Kin ganni nafi awa nawa ina lallaɓa ƴar rigimarnan amman haƙona yaƙi kai ga ci" Yaran na kalla nace. Amira kama hannunsu, ga ɗari biyu kuje ku siyi wara kuci ko? Kafin kayanmu su ƙaraso yarana na siya muku kaya masu kyau da tsada. Harda Hafizu a washe baki. Suna fita saina dawo da hankalina kan Hafizu. Ina saurarenka" "Iyabo kinsan kun tafi kun barni akan baifi wata ɗaya nima yayi mun ragowa in tafi Canada ba. An samamun aikin da bamu san wanne iri bane. To ko bayan tafiyarku saida muka fi wata huɗu kafinma muka tafi. Tsaiwa kwatanta azaba da wahalar da matasa ƴan cirani suke sha a ƙasashen waje ɓata bakine Iyabo, abun duk gidogace ruɗune. Shekarata biyu a daddafe na dawo da kuɗin da bai taka kara ya karyaba, banda jinyar jiki dana sha. Dawowata ke da wuya ina zuwa ƙauyenmu sai mahaifiyata take nina mun Farida tace ai an ɗaura aurena da'ita. Kinsan mutanen ƙauye gani suke yi wani kuɗi nayi. Ni kuma a cikin kuɗin da nazo dashi da ƙyar na ƙuƙuta harda bashi na sai ɗan ƙaramin gida mai ɗakuna uku rak. Amarya ta tare a ɗaya, ɗayan nazo wajen Hajiya na karɓi yarana suka tare a ciki, ɗayan kuma na kulle mata a matsayin ɗakinta. Shine fa taƙi fahimtata ca take wai ita in saketa kawai. Yanzu taya zan saki uwar Ƴaƴana uhm Alaja Iyabo ki duba zancena sabida Allah kiyi mun adalci" Jikina yayi murus hankalina sai naji ya tashi. Lallai in har haka ta faru da Uwani. Ni kam ina cikin goma sha biyu. Uwani duk sabida rufin asirinsu ta tafi wannan ƙasa, amman jibi abinda ya biyo baya kafin dawowarta. Ina kuma gani da ko kalmar so Yaya Hamma bai furtamun ba?" Da ƙyar na yakice tunani na sauke ajjiyar zuchiya nace. Shikenan Hafizu zata dawo ɗakinta amman dole sai dare. Sai dai da yamma ni da Ummi zamu zo mu yi mata jere" Baki ya washe yana dariya ya miƙe. Har fa ya kai bakin ƙofa ya dawo. "Alaja Iyabo ni kuwa kayan naku masu isowa har dila nawa ne?" Hararar da Uwani ta zabga mishi ce yasa yayi firgigit ya fice yana dariya" "Kikace zan koma Iyabo? Ni wallahi da naso in haƙura da Hafizu. Duk wannan tatsuniyace fa ya baki ɗan iska marar mutunci" A'a Uwani ki koma kan ƴaƴanki, ki riƙe sana'arki ki kula da kanki da Ƴaƴanki. Ki godema Allah ba mazinaci Hafizu ya zama ba, kuma ki gode Allah baki mallaka mishi dukiyar da kika sha baƙar azaba wajen tarata ba. Yanzu dai ki taso muje mu sai kayan ɗaki na gani a faɗe." Harara ta gallamun. Nayi dariya nace. Zaki bari matarshi ta rainaki ne, ke da kike Hajiya? Uwani kiyi haƙuri dan Allah karma ki nuna ma kishiyarki wai kinji zafin abinda suka aikata miki." "To Shikenan Iyabo. Na ɗauki shawararki. Amman sisina bazan iya kashewa akan Hafizu ko matarshi ba wallahi in tsirara zasu yi yawo sun dade basui ba. Muje ni dalla" Fitowa mu kayi, daidai Iyaa itama ta fito. "Ina zakuje kuma?" Zan raka Uwani ta siyo kayan ɗakine da daddare zata koma gidanta" Hajiya ta taɓe bakinta tace. "Sun gama tata ɓurzar kenan? Ai haƙuri dama dole za,a yi daga ƙarshe, kindai ga halin mazan dai. Wannan ya isheki hankali sai ki tattala dukiyarki kiyi abinda zai fissheku. In da ke kaɗai kike da Hafizu to yanzu ku biyu ne. In da ƴaƴanki ne kaɗai ƴaƴa yanzu suna da Ɗan uba harda wani cikin" Ni dai jikina sake mutuwa murus yayi. Zuchiyata saita shiga cikin taraddadin abinda ni kaina zanje in tarar a ƙauye. Ni dai har muka isa shagon saida kayan katako da Uwani da ƙannenta mata biyu da suketa mana biyayya mu ga hajiyoyi. Kado da sib da mudubi kawai muka siya, sai labule da makeken kafet mai taushi. Kayan kitchen kuwa ɗan tsakura tayi sabida nanda wata ɗaya kayanmu zasu iso. Ni da ƙannenta ne muka wuce gidan, ita kuma ta wuce kasuwar kurmi ɗan siyayyar kayanmu na mata. Gidan wani irin gantalallen gidane ginin laka, ko filasta babu a tsakar gidan, datti da shara takota ina. Hafizun yana zaune a ƙofar ɗakin da ya kasance na Uwani. Amarya kuma sai wanki take yi ga ciki a jikinta ga yaro a ƙofar barandar ɗakinta a kwance." Hafizu masu motar kaya suna waje ka taimaka musu. Amarya barka da gida" Na faɗa a tare. Babu yabo babu fallasa ta gaishemu kana taci gaba da wankinta. Niko ƙare mata kallo na shiga yi tsab, in banda abun ɗa namiji ni dai banga ta inda za'a haɗa Uwani da kishiya irin wannan ba. Ko da yake ita mace duk lalacewarta da ƙauyancinta tana da tata baiwar da Allah ya huwace mata. Dan a hakam saita zama zarah a zuchiyar Hafizu. Shigowar su Hafizu da sib me murfi huɗu ce tasa na dawo hayyacina. Amarya a ara mana tsintsiya dan Allah " Ɗan murmushin yaƙe tayi tace. "Wallahi gidan bani da tsintsiya. Nima da tsumma nake sharar ɗakina" Ai sai na rike baki tsintsiyar laushi ta nera goma ace ta gagari yarinyar mace. Kuɗi na ciro na ba Ummi nace. A siya tsintsiyar laushi data zabori, sai abun kwashe shara, da kwandon shara. Ki siyo kwandon sharar babba da ƙarami, a siyo omo." Nan da nan ummi taje ta siyo dake layin cike yake da shaguna. Tas muka wanke ɗakin muka koro ruwan tsakar gida. Amarya ta bamu tsumma muka goge ɗakin. Muka shirya ɗakin Amarya tas da taimakon Hafizu sai ɓare_ɓare yake yi har ciwo yaji garin shigar da madubi. Amaryarshi sai harara take doka mishi. Ummi nasa ta share tsakar gidan ya dawo saiti, nasa suka wanke ƙazamin banɗakinsu mai zarni da warin masai. Bamu muka bar gidan ba sai biyar na yamma. Zuwa bayan Isha na raka uwani gidanta. Muna shiga ɗakin ta kalli ɗakin ta sharce hawayenta tace. "Iyabo ni kam zan sai gida madaidaici kamar wannan ni da yarana saimu koma. A ɗakinnan ta ina zan soma kasuwanci, banga inda zan ajjiye dilolina in sun ƙaraso ba. Nifa Iyabo haƙurin da zanyi a gidannan na kafin a samamun gidane in siya" Dafata nayi. Uwani babu laifi dan kinyi hakanma. Nima kuma na goyi da bayan ki sai gidan naki ki ware kan ki. Ni zan tafi ƙauye gobe sassafe, in dilarmu ta iso nasan zaki karɓo mana ki ajjiye mun tawa a wajenki. Ni kaina jikina yana bani zanje in tarar Yaya Hamma ya cika gidanshi da Mata, uwani gashi Allah ya jarabceni da tsantsar sonshi. Tsaki tayi tace. "Ni bawai Hamma bai cancanci ki soshi bane. Ni gani nake kashe rayuwarki kawai zakiyi in dai Hamma kike son ki aura. A wannan ƙungurmin ƙauyen kike sha'awar rayuwa alhalin na ƙauye suke fitowa birni Iyabo. Kiyi nazari, ki kuma auna Hamma da Salim, sannan ki yi nazari mai zurfi kafin ki je ki faɗa abinda zai zame miki matsala. Rayuwarki ce kece zaki zauna" Da wannan mu kai sallama na koma gida. Nima da wannan nake cewa daku sai gobe in Allah ya ara mana rayuwar. MRS BUKHARI 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230[8/28, 12:22 PM] +234 803 969 6400: NAMA YA DAHU... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 17 Ina daf da shiga gidan wan mahaifina Alfa Kulle dan in mishi sallamar gobe zan koma ƙauyenmu. Sai naji muryar Burodami Debisi. "Iyabo tun magriba nake jiranki a tsakankanin gidajannan biyu. Dan nasan gobe zaki tafi wajen Hamma. Nayi imani da ace yasan kin dawo da yanzu yana naniƙe dake" Cikin kishi da jin zafi yake maganar. Ni dariya ma ya bani sosai. Sai da na dara tukunna kana nace. To mu shiga inma Alfa sallama in mun fito sai muyi magana. Shi kuma Alfa muna shiga bayan na karanto mishi inaso zan koma ƙauyanmu kamar jirana yake sai yace. "Ba zamu saka miki idanu ba, sai kuma ki kawo maganar aure a gabanki hakanan. Na baki wata biyu ki fito da miji, in baki fitar ba zamu fitar miki. Dan da ace Toye yana da ranshi ma ko Saudiyya da kika je ba zai bari kije ba. Tun kafin jama'a su soma miki wani irin kallo gara ki fitar da mijin aure" Kaina a sauke nace. In sha Allah kafin lokacin yayi zan fitar Baami." A gidan muka ci abinci a cikin ɗakin Iyaa Ramata." "Kin tuna da wancan gadon da in kun mun lefi ke da Bose kuke shigewa?" Cewar Debisi daya samu saken daga ni sai shi a ɗakin. Dariya kawai nayi inacin amala. "Yaya batun aurena dake ya kwana Iyabo? Tunda Allah ya dawo dake ya kamata muyi magana tsayayya" Rai na haɗe nace. Har abada ni da kai ba zamu zama mata da mijiba, muna nan a matsayin Yaya da ƙanwarnan. Na riga na faɗama tun kafin in tafi. Ina ni ina haɗa miji da Soja?" Murmushi yayi mun har yana gyaɗa kai. "Lallai yarinyarnan bakin ki ya buɗe. Nifa wallahi da gaske nake yi, da kinsan irin yadda sonki yake nuƙurƙusar zuchiyata nayi imani da tuni kin ceci ran ɗan uwanki" Kallon dana watso mishi bansan na iyaba, a mafarki banyi zaton zan iya mishi makamancin wannan kallon ba. Amman sai gashi nayi. Hannuna na tsame tsam a abinci na ficewara na bar gidanma baki ɗaya. Koda na shiga Yemisi na zaune tana zaman jiran mijinta su koma gida. Ban jima da shigowa ba sai gashi, ko shigowa baiba cikin ƙailula yace ta fito su tafi, gaga_gaga yai ma Iyaa sallama. "Iyabo wai menene tsakaninki da Hamma? Dan naga damuwar da yayi akan lamarinki abun yayi yawa, yafi ƙarfin ace ƴan uwantakane kawai. Duk sanda Daso zata zo bayan tafiyarki dashi ake zuwa. Shine nake son jin ina fatan ba tallar nono zaki koma yi ba, ki dawo mai sharar kashin shanu da dafa madara. Ai in abune mai daɗi da ba haka ba. Rayuwar matan fulanin daji cike take da bauta, matan da yawa da wannan tallar nonon suke ciyar da gida, su kuma mazan suna bin jeji_jeji suna kiwon shanunsu. Ke irin rayuwar da mahaifiyarki take yi irinta zaki jefa kanki aciki? Kwanaki can da Debisi yaje ya tarar da Daso ba lafiya ga ƙaninki Amaduyal ya dawo daga inda suke fita kula da shanu ga kuɗi a jikinshi a kaita asibiti ubansu ya hana. Sai Debisi ne ya dinga jigilar sai mata magani shima a ɓoye ana bata. Irin rayuwar da kike sha'awa kenan ko?" Illahirin jikina sai naji yana rawa da ƙyar nai kokuwa da harshena wajen sarrafashi. Iyaa ni bazan yi tallar Nono ba. Kuma Hamma shi yana fita aiki a birni masinja ne a ma'aikata bai dogara da iya kiwon shanu ba, mijin Baɗɗo yafi fita da shanun.Sannan.... "Otito ( ya'isa haka) ki dai yi tunani ki kalli uwarki a matsayin mudubi zaki gane mai nake nufi. Rayuwar ƙauye sai ƴan ƙauye madamar suma sun fito ko ziyara dan dole suke zuwa" Ta dinga mun kwatance iri da kala. Da waɗannan tunanin gari ya waye damu. Gaga_ gaga bayan nayi wanka nayi Sallah, saina saɓi akwatina. Nayi sallama da mutan gidanmu sai tasha. Motar Adamawa saura Mutum uku ta cika, nayi zamana ina ta aikin tunanin yadda rayuwa zata kasance inna auri Yaya Hamma. Sai wani shashe na zuchiyata ya tunasar dani cewar "Ai masoyi masoyine imma a birni imma a ƙauye. Zaman aure nutsuwa ake nema, soyayya babu ruwanta da ɗan birni babu ruwanta da ɗan ƙauye. Ban rufekuba na faɗa muku ni Allahn da yayini in inason abu idanuna rufewa yakeyi bana ji ko gani akanshi. ( Ina maƙiyan Hamma kuna dai jin tsuntsun soyayya abinda take faɗe) Wannan tunanin saiya saisaitani, yayinda motarmu ta saitu a hanya ita kuma, mukaita ratata gudu. Bayan gushewar sakanni, mintuna, awanni sai gani a Jere Banyo cikin yardar Ubangiji sai dai galabaita da nayi. Hanyar shigowan tananan inda na barta babu abinda ya canja. Gidan Yafendona na nufa kai tsaye da sallama na shiga. Harira kaɗai matar Jatau ce a gidan itama da halama dawowarta kenan. "Jabu use kece a garin naraba da baƙin larabawa" Da kwaɓaɓɓiyar Hausarta tayi magana Nice Hari, Yafendo bata dawo tallan nono bane?" Sai naga fuskarta ta sauya daga murnar ganina izuwa alhini. "Hmmm Yafendonki tana gidanku wajen Baba Daso jikinta yayi tsanani sosai yau dan ance batasan wanda yake kanta ba ma" Daga tsayen na saki akwatina iyakar jakar hannuna da kuɗaɗena suke ciki na sake mata kyakkyawan riƙo. Sauri_ sauri gudu_gudu na dinga haɗawa dashi zuchiyata tana fat_fat harna iso ƙofar gidan. Dawowar Baffan su Boɗɗo daga kiwo kenan. Yana tsaye yana kora shanu ciki. Ni kuma na rakuɓe a gefe ina jiran garken shanun su gama shiga, mu gaisa in kuma roƙeshi inason ganin Dada. ko kallon inda nake baiyi ba har sai da shanun suka gama shigewa ya kalleni. "Kar ma kice gidannan zaki shiga. Na haramta miki shiga cikin gidannan ɓilgel (Yarinya) Dan haka kiyi maza ki bar wajennan. A guje wani saurayi ya fito yana faɗin "Baffa Dada zata mutu jijjiga take yi" Jin haka yasa na kutsa kai da gudu cikin gidan, da kuma ƙarfina dan idanuna ya rufe sai ganina nayi a ɗakin Dada a tsaye. Baffan yayi yinƙurin hanani shiga gidan, da ƙarfin tsiya na bangajeshi nayi shigewata Tozali nayi da sanyin idanuna yana tallafo kan Dada daga kwancen da take duk ya kiɗime. Wata ajjiyar zuchiya ya sauke. "Adda Jabu ashe kin dawo, gashi inzo kin samu Dada a wani irin mawuyacin hali rai a hannun Allah" Cewar Baɗɗo data ƙarashe maganarta da kuka. Hannunta na riƙe nima ina kuka ƙannena suka tawo gareni suna neman kafaɗar da zasu ɗaura kansu suyi kukansu. Mijin Baɗɗone yace. "Amaduyal dole fa akai Dada asibiti" Inajin haka nace. Anemo mota maza zamu kaita asibiti yanzu" Da sauri na ƙarasa kusa da'ita da ƙyar take jan numfashinta Yaya Hamma yana goge mata fuska da jiƙaƙƙe tsumma dan zazzaɓin jikinta yayi tsanani ainun. Sannu Dada" Carab tana jin muryata Allah cikin ikonshi saita riƙe mayafina carab kamar wacce zata gudu. Kukanmu kawai ke tashi a ɗakin har su Amaduyal suka shigo da sauri Yafendo Mahaifiyar Yaya Hamma tace. "An samu motarne?" "Ansamu malam iro zai kaita a motarshi. Ina fita shi kuma ya kawo kaya yana saukewa," Kintsa Dada akayi bayan mazan sun fita daga ɗakin. Dani da Boɗɗo ne muka tarairayota jikinmu su Yafendo na taimakawa har muka fito. Kishiyoyin Dada su kai ca a kanmu. "Ke Boɗɗo ba Baffanku yace kar a kuskura a fitar da'ita gidan ko wanne me magani ba?" Yafendo tana sharce hawaye tace. "A wannan gaɓar da Yaya Daso take buƙatar taimako, bama buƙatar sahakewar mai nagge. Mujenku Jabu" Har munje bakin ƙofar fita muka jiyo Baffa a bayanmu yana cewa "Indai kuka nuna kun fini iko da Daso, to in kuka fitar da'ita a gidannan to na saketa saki ɗaya. Ku kuma Cubu ku wuce cikin gida ƴan gatan uwa." Wani baƙin cikine ya dirarmun a ƙahon zuchiyata babu shiri na runtse idanuna, yayinda hawaye masu zafi sukaita shatatomun. Amaduyal da Hamma ne suka amshi Dada suka fice da'ita. Yafendona tana kuka tace. "Me nagge kanka ka cutar ba Daso ba. Kuma ka sani sai Allah ya tsayar daku ya fitarma da Daso hakkin zaluntarta da kayi a rayuwa. Ga gidanka nan, ƴaƴanma gaka gasu ƙila sune zasu zama jarabawarka. Sannan ka shirya tsab tunda bakwa aure dole ka dawo mata da garken shanunta." Da gaggawa muka fita a cikin gidan, Yaya Hamma ni yake kallo idanunshi sun zama jawur kamar garwashin wuta. Namadi ne yace. "Yafendo ku shigo mu tafi numfashinta tuni ya ɗauke fa" Bayan akori kurarnan muka shiga dukkanmu. Boɗɗo tana goye da wata fara kyakkyawar yarinya mai gashin fulani a kayinta. Sai dai ita uwar duk kazanta da rashin zama a waje ɗaya ya komaɗar da'ita. Kaina na sauke ƙasa ina ma Dada adda'ar Allah ya bata tsawon rayuwar da zata ji daɗi taci ribar ƴaƴa. Cikin gaggawa muka wuce babban asibitin gwammati dake cikin garin Adamawa, sun so mu tsaya a asibitin Girei, ni kuma nace mu tafi babban asibiti kawai, ai kuwa muna shiga na shiga cikin asibitin da hanzari dan neman agajin ma'aikatan jinya. Yaya Hamma da Amaduyal kuma suka kinkimo Dada zuwa wani dogon falo. Ma'aikatan jinyarnan da suka ga mu fulanin Daji ne sai suka banzatar da lamarinmu ga Dada ko numfashi bata yi, sai da muka yanki kati muka biya kuɗin gado kana suka sauraremu. Ward ɗin mata aka kwantar da Dada, sai dai bata samu gado ba, a katifa aka kwantar da'ita. Kasancewar ɗakin cike yake dam da marasa lafiya, rabi da kwatan majinyatan ɗakin fulanine. Wani dattijon likitane yazo kan Dada, dubanmu yayi yace. "Ku duka yaran majinyaciyarne?" Yafendona tace. "Duk yaranta ne, mu kuma ƙannenta ne" Kai ya girgiza yace. "Allah sarki, to ku ɗan dakata daga waje zan dubata, inna gama sai ku dawo ko? Amman zaku iya komawa gida ku ɗebo kayan jinya dan naga jikin mahaifiyar taku da tsanani riƙeku zamu yi. Ku tawo da bargo babba na rufa, dan zata iya jin sanyi cikin dare, wannan na asibiti bashi da kauri" Ni dai da ƙyar nake ɗaga ƙafata sabida yanda naga halin da Dada take ciki, da irin ƙanjamewar da tayi duk saina sare. Zama muka yi a bencin da aka tanada domin zama. Babu me cewa da kowa komai. Ni dai duk ɗagowar da zanyi saimun haɗa idanu da Yaya Hamma. Hankalinshi gabaki ɗaya yana kaina ko ƙibtawa bayayi. A tsaye yake yayi tsaiwa irinta fulani, irin tsaiwar da suke yi da ƙafa ɗaya, ɗayar ƙafar sai su ɗaurata akan ɗayar. Fararen kaifafan idanunshi sai yawo suke yi a jikina.." "Jabu yaushe kika dawo, ya kika baro jama'ar makka?" Cewar mahaifiyar Yaya Hamma. Shekaran jiya jirginmu ya sauka a Legos, jiya muka shiga Kano Yafendo. "Allah sarki sai kika dawo kika tarar da Adda Daso cikin jinya. Shekararta guda munata fama. Hamma shi yaita jigilar nemo mata magunguna ƙauye_ƙauye bai taɓa gajiyawa ba. Babu abinda zamu ce dashi sai dai muce Allah ya bar zumunci. Cewar Yafendona. Sai naji zuchiyata ta sake nitsewa a so da ƙaunar Yaya Hamma. Wanda zaima mahaifiyarka wannan hidimar ai dole kaji ka soshi. Murmushi nayi nace. Allah sarki. Yaya Hamma Allah ya saka maka da Alkhairi. Allah ya bar mana zumuncinmu. Boɗɗo kema ciwon kika yi ne naga duk kin fice a haiyacinki?" Na tambayeta cikin kulawa. "A'a Adda yanayin canjin rayuwane kawai, da kuma ciwon Dada,. Yaya Amaduyal wannan itace yarmu Adda Jabu" Tana faɗar haka Amaduyal ya rusuna kanshi a ƙasa yai mun sannu da zuwa, sai murnar ganina yake yi. Nima naji daɗi sosai dana sake kasancewa tare da dangina.Yaya Hamma duk wannan maganar da akeyi baiyi ko tari ba, sai ido kawai da yaketa binmu dashi. Likitan daya shiga duba Dada ne ya fito. "Mutum biyu daga cikin Yaran Daso su biyoni a baya" Yafendo sai ta nuna ni, ni da Yaya Hamma muka bishi zuwa ofishinshi, ya bamu wajen zama. "Tun yaushe baiwar Allah'nnan take cikin wannan halin kuka barta a gida saida ciwo ya cinye jikinta sannan zaku kawo mana ita? Tazo ta mutu a hsnnunmu ku ɗaura alhakin kisan a kanmu" Yaya Hamma ne yace. "Dakta ciwon zata kai shekara ɗaya da rabi haka tana yi. Amman a tsaitsaye da yin tsananinshi baifi watanni shidda ba. Sai an ɗagata sai an kwantar da'ita. Munyi magunguna gargajiya da yawa ba haka muka zauna ba" Wannan Dakta ya zare tabarau ɗinshi daga idanunshi. Ni kaina jin tsayin lokacin da Dada ta ɗauka tana jinya ya ɗagamun hankali, tausayinta ya sake ɗarsuwa a zuchiyata ai saina fashe da kuka ina salati a hankali. "Jabu kiyi shiru, kuyi haƙuri in sha Allah Dada zata tashi. Ƙarshen wahalarta a gidan Baffa yazo tunda ya rabu da'ita. Dani dake zamu iya riƙe Dada mu bata farin ciki. Dakta a faɗa mana abinda yake damunta." "To abinda yake damunta suna da yawa. Na farko shine hawan jini, dan jininta ya hau sosai, babban abinda yake damunta cutar Rawaya ce, sabida tsananta da yayi ya haifar mata da ƙurajen a hanjinta, ma'ana yaci hanjinta sosai da sosai. Dole tana buƙatar ai mata aiki ciwo kun bari yaci jikinta ainun. Akwai buƙatar ai mata ƙarin ruwa, babu ruwa babu jini sosai a jikinta. Kunyi sake da yawa, Mama na da tsawon rai ne shi yasa har Allah yasa ta kawo yanzu da ranta." Ni dai hawaye kawai nake zubarwa na tsantsar tausayin Dadana. Allah sarki baiwar Allah damo sarkin haƙuri kenan. Yaya Hamma yace. "To Dakta wanzu me ake buƙata daga ɓangarenmu?" "Akwai buƙatar kuɗi, sannan akwai buƙatar ku bata jini a ƙara mata. Da zaran mun gama duk gwaje_gwajen daya dace in sha Allah zamu sanar daku lokacin da za'ayi mata aikin. Bazai wuce jibi ba Ku dai ku tanaɗi kuɗi." Kai Yaya Hamma ya dafe da hannunshi. "To Shikenan, a bata jinina a saka mata Dakta" Dariya Dakta yayi yace. "Za'ku je lap dai a tabbatar da ingancin jinin, in yayi daidai da nata sai a ɗiba. Amman sai dai kuje ku biyu ko uku, dan leda shidda muke buƙata na jini." Tare muka fito, Yaya Hamma ya kirayi su Amaduyal suka wuce lap domin a aunasu. Ni kuma a sanyaye naima su Yafendo bayanin halin da Dada take ciki. Yafendo ina ganin ko zaku tafi gida, ni da Boɗɗo saimu dinga kwana da'ita. Asibitin akwai sanyi zai iya damunku, kuma gida Babu kowa." Kafin suce wani abun saiga Baffa Musa da Yafendo A'i hankulansu duk a tashe. "A'i am kina fama da kanki ai da kin turo Jumare yazo ke ki huta a gida. Ga dare harya rufa" Cewar Yafendo Kaɓoji. Hawaye Yafendo A'i ta share da mayafinta. "Zuchiyata ba zata samu nitsuwa ba. Yadda labarin yazo mun. Su Cubu na gidan Yaya Musa Mai Nagge ya korosu suma bayan tafiyarku. Hakan bai mishi ba ya samu Yaya Musa yake faɗa mishi wai Jabu zata gani duk abinda ya faru da'ita shine. Sannan ga yara mu mu riƙe tunda mun nuna mun fishi iko. Abun dai babu daɗi sam" Baffa Musa yace. "Ku ajjiye wannan maganar a gefe. Ke Jabu yaya jikin ita Dason?" Yafendona tace. "To jikin nata sai adda'a Yaya" Ta labarta musu abinda Dakta yace. Baffa Musa sai ya buɗe baki yana maganar su ba za'aima Dada aikiba mutuwa akeyi a asibiti, su kaza su kaza. Kuma su Yafendo suka goyu bayanshi akan hakan tare da yanke hukuncin zasu mayar da Dada gida ayi mata na Hausa. Ai saina fashe da kuka na zube ƙasa. Baffa am dan Allah kuyi mana rai Dada tana buƙatar jini da ruwa. Tana buƙatar kulawar asibiti tunda ance babu irin na hausan da ba'ayiba. Ku bari mu jarraba na asibitin" Ganina a ƙasa yasa Boɗɗo itama ta tsugunna muka ci gaba da basu haƙuri. Kundai san halin iyayen namu Fulani da taurin kai, da kuma ƙauyanci. Baffa Musa sam yaƙi yarda gashi shine mai faɗe aji a dangi kasancewarshi babba. Ni dai na koma saman kujera sai kuka nake yi Yafendo A'i tana rarrashina. A haka su Yuguda suka zo suka samemu. "Daga ina kuke Yuguda?" Buɗar bakinshi yace. "Wata likitace wai zata kwashi jinina ni na taɓa jin yadda akayi haka Baffa? Yaya Hamma yana kwance tana zuƙe mai jini wai za'a sama Dada, Amaduyal ma Yaya Hamma yace dole sai ta zuƙi nashi. Ni gaskiya bazan iyaba." Banga laifin Yuguda ba, rashin ilimi da rashin wayewa ke damunsu. "Jabu kinga duk abinda zuwa asibitinnan ya jawo ko? Mu fa a kan zuriyarmu babu wanda waɗannan mayun suka taɓa mana. Bama zuwa asibiti mu. Yuguda mu je ka kaini ɗakin shan jinin maza." Da sauri na riƙe babbar rigar Baffa. Dan Allah Baffa ka tsaya kaji. In ba'a sama Dada jininnan ba mutuwa zata yi" Sai yayi dariya yace. "Yarinya muna da maganin ƙarin jini namu na gargajiya da muke sha tun iyaye da kakanni. Daso ba za'a ƙara mata jinin maita ba." Muna cikin wannan badaƙalar wannan Dakta dake lura da Dada yazo zai wuce yaji abinda muke tattaunawa dake mutumin kirki ne kuma shima bafulataninne sai ya gaiyacemu ofishinshi. "Baffa Musa kamar yadda naji yara na kiranka ko, nasan ba lalle ka ganeni ba. Ubale ne ƙanin Ilyasu gare_gare." Da jin haka Baffa yace. "Ilyasu gare_gare abokinmu da yake ɗaya daga cikin mutanen da turawa suka ɗiba zuwa ƙasar waje dan suyi boko" Dakta yayi dariya. "Shifa Baffa Musa. To ni ƙaramin ƙaninsune wannan wanda kuke kora in zaku dandali. Wannan wanda bayan kaci shaɗin aure yake rakaka zance" Ajjiyar zuchiya na sauke jin abinda Dakta yake ce da Baffa Musa. Nasan ko babu komai zai iya shawo hankalinshi ya bar Dada a asibiti a nema mata lafiya. "Hahaha Ubale baka da mantuwa gaskiya. Yanzu shi Ilyasu gare_gare yana inane?" "Yana ingila da iyalanshi acan yake aiki shekara ashirin da biyar kenan." Baffa yace. "Allah sarki. Kai ka tura yara wai aje a tsotse jininsu Ubale? Marar lafiyar fa Daso ce ƙanwata kafa santa. Kaga ga A'i, ga Kaɓoji, ga Jabu. Waɗannan biyun yaran Dason ne, wannan kuma yaron kaɓojine." Nan Dakta ya dinga yima Baffa Musa bayani cikin hikima da dabaru irinna masu gogewa. Da ƙyar da suɗin goshi Baffa Musa ya amince yace a bar Dada a asibitin. Ajjiyar zuchiya na sauke mai ƙarfi. "To Alhamdulillah Baffa Musa, in sha Allah ba za kuyi dana sanin zuwa asibiti da'ita ba. Amman ku zaku koma gida mutum biyu sai su zauna da'ita a cikin ɗakin. So samu da namiji ɗaya ko za'a buƙaci wani abun." Baffa yace. "To Shikenan Jabu da Boɗɗo tunda sune masu jini a jika sai su zauna. Hamma ya zauna dasu ɗan baɗo dan na lura kamar ƴar gida za'ayi da Jabu" Sauke kaina nayi da sauri ina ɗan murmushi. Da haka muka fito a ƙofar ward ɗin su Dada muka ga su Hamma suna zaune a benci. Tare duk muka ɗunguma ciki, Dada na kwance ana mata ƙarin ruwa. Fuskarta tayi fayau. A gurguje suka dubata su kai mana sallama. Yafendo a tawo mana da bargo da taburma gobe in za'a kawo mana abincin safe. Akwatin kayana yana wajen Hari ki karɓa. Dafa kafaɗata tayi tace. "Allah yayi muku albarka, Allah ya baku ladan jinya. Gobe Daso zata tawo muku dashi, ita zata yo abinci daga gidanta ta kawo muku. Boɗɗo ki kunto goyon yarinyarnan asibitinnan da akwai sanyi kuji da kanku. Ita yarinyar tasha nonon shanu tunda akwai masu shayarwa." Boɗɗo ta sunto ƴarta Baban ƴar ya amshe abinshi. Yaya Hamma yace. "Jabu ku kula da Dada bari in kaisu Baffa tasha. Daga nan zan tawo muku da abinci" A dawo lafiya mu ka yi mishi. A lokacin ƙarfe kusan takwas na dare. Banyi la'asarba ga magriba da isha, ni sai yanzu na tuna. Boɗɗo bari inje in nemi wajan alwala, ke ki zauna inna dawo sai kije kema kiyi." Fita nayi da tambaya da kwatance na je wajen yin alwala da kama ruwa. A wata katuwar rumfa na hango mata suna sallah nima na shige cikinsu na rama sallolin da ake bina. Na jima sosai ina kai kukana ga Allah, tare da neman tsari a wajen Allah game da furucin Baffa a kaina na dukkan abinda ya sameni shine. Gaisawa nayi da matan dake cikin rumfar. Wata bafulatana tace. "Ai ɗakinmu ɗaya gadonmu na kusa da naku. Marar lafiyar mahaifiyarku ce?" Na dubi matar a girme kamar ba zata girme mun ba. Nace da'ita. Allah sarki, mahaifiyarmu ce" "Allah ya bata lafiya. Nima mahaifiyata nake jinya mun kai tsawon wata uku a asibitinnan muna jinyarta. Kinsan yanayin jikin tsufa, ya haɗu da ciwo" Kai na gyaɗa nace. Hakane kam. Allah ya basu lafiya baki ɗaya. "Ni sunana Sumayya, muna zaune a Girei kefa?" Sunana Jabu. Mu a ƙauyen Jere Banyo muke" Tare muka koma ɗakin jinya da Sumayya, muna tafe tana jana da hira har muka iso inda Dada take kwance. Da Boɗɗo suka gaisa. Nina na ƙarasa naima mahaifiyarta Yaya jiki, tana zaune tana shan kunu. Komawa nayi kusa da Baɗɗo. Dada bata motsa ba Baɗɗo tunda na tafi?" Shiru Baɗɗo bata ma san inayi ba hankalinta baya asibitinnan da halama yayi nisa. Na lura bayan ciwon Dada akwai matsalar dake nuƙurƙusan Baɗɗo shine ma dalilin ramarta. Kafaɗarta na dafa sai tayi sauri ta kalleni. Komai yayi tsanani maganin yana ga Allah. Baɗɗo je kiyi Sallah ki dawo ki sanar dani damuwarki, zan taimaka miki ko da da adda'a ne." Bata ce komai ba ta fita. Ni kuma na ƙurama Dada idanu sai numfashi taie ja tana saukewa, ga wani irin sanyi da akeyi, damma ɗakin da jama'a sosai gadajen marasa lafiya zasu iya kaiwa guda talatin. "Jabu ga abinci kuci naga kamar ba'a kawo muku abincin ba tukunna ko?" Na jiyo muryar sumayya a bayana da kwanon samirah a hannunta. Nasa hannu na amsa. Mun gode Sumayya. E ba'a kawo mana abincin ba tukunna dai, nafa gode. Murmushi tayi mun tace. 'ai mun zama ɗaya Jabu, ki saki jiki duk abinda kike buƙata ki tambayeni kawai." To Shikenan Sumayya." Kwanon abincin na ajjiye a gefen katifar da Dada take kwance. MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI. 09153081057 Ga masu san magana dani kai tsaye ta whatApp ga number na Masoyana sunata mun ƙorafin babu number na a jikin littafi kuma suna son muyi zumunci, ƙorafi ya ƙare. Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230 [8/29, 6:09 PM] +234 803 969 6400: Ku Shashe takaicinku da wannan page ɗi. Ƴan bati an gaisheku inata sauraren comments daga gareku kuma ba'a barku a baya ba. NAMA YA DAHU.... ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 19 Maraɗi Gwadabe Yana fitowa daga ɗakin Hadiza ya sauke ajjiyar zuchiya sassanya. Tsaki yaji an doka daga gabanshi, ɗagowar da zaiyi yaga ashe Baba Asshi ce a tsaye da yaranta da matansu a tsakar gidan suna ƙus_ƙus. "Ina wuni Baba Asshi?" In kun tanka Baba Asshi ta tanka. Saida ya wuce ta sake jan wani dogon tsakin, kanshi kawai ya gyaɗa yana fata da burin kar a samu irin wannan rarrabuwar kan a nashi gidan. Da sallama ya shiga ɗakin Amarya Shafa. Tana zaune akan kujera tasha adon atamfarta baƙar macce ƴar leda. Bakinnan nata yasha janbaki raɗau sai sheƙi yakeyi. Komai zaune yake daram a muhallinshi. Da sauri Shafa ta miƙe ta tawo da sassarfa izuwa wajen mijinta. Isowarta ke da wuya ya haɗe jikinshi da nata ya riƙeta gam. Ajjiyar zuchiya ya sauke mai ƙarfi a zuchiyarshi yace.."Lallai aure ni'imace akwai hikima a auren mata biyu, shi yasa ubangijinmu ya umarcemu da somawa da biyu madamar zamuyi adalci. Ko wacce mace da irin ƙamshinta, taushin fatarta, kalaminta, Sannan da irin baiwar da Allah subuhanahu wata ala yai mata. A wannan daren Amarci Gwadabe ya gwangwaji Amarcinshi lami lafiya kuma Alhamdulillah Shafa ta kawo cikakken budurci marar kokonto a cikinshi. Tana kwance a ƙirjin mijinta tana baccin daɗi da wahala zuchiyoyinsu fes. Ta ɓangaren Hadiza kuwa tana kwance tana lissafe lissafe gami da hasaso abinda bazai taɓa bata kwanciyar hankali da nutsuwa ba. Dan a wannan daren sai da ta dinga tambayar kanta to waima me yasa ta amince da Auren Gwadabe ne ma?" Nasihu da surruka, da dabarun zama da kishiya, da zama tauraruwa a idanun miji da Baba Fhatsima ta karanto mata, shi ya sake faɗi mata. Wasu zafafan hawaye suka gangaro suka wanke mata kumatunta. Zurub ta miƙe ta faɗa banɗaki ta ɗauro alwala ta koma ɗakinta. Ta maye gurbin tunane_tunanen da basu da amfani da yin sallolin nafila tana miƙa kukanta ga Ubangiji kan ya sassauta mata kishin dake zuchiyarta. Yaa kuma kareta da cutar da abokiyar zamanta koda da furucine. Ya ɗaga daraja da kimarta a idanun mijinta. Haka ta dinga sallah tana adda'a, ai kuwa saida taga bacci yana shirin kayar da'ita sannan ta kwanta. Ta kuwa samu bacci mai nutsuwa kuma nannauya. Asubar fari ta miƙe ta nufi kitchen. Dai_dai Shafa itama ta buɗe ƙofar ɗakinta ta fito kitchen. Idanu suka haɗa duk da dai akwai duhu amman sunsan juna suke kallo. "Yaya barka da asuba" Shafa ta faɗa tana ƙoƙarin buɗe kitchen ɗinta. "Yauwa barka dai Amarya mai maganar suger. Ya kwanan angon naki?" Shafa tayi murmushi ta ɗan sauke kanta ƙasa bata ce komai ba dai. Kitchen Hadiza ta faɗa tana murmushi, amman a baɗini zuchiyarta ma bugawa yake yi, hatta hannayenta sai taji suna rawa kakakar_kakakar. Cikin zuchiyarta tace. "Kishi bala'ine. Gaskiya mana a gidanmu aka kasa samun dedeto. Ashe haka kishi yake da tasiri mai girma?" Hawayen dake shirin zubowa a idanunta ta mayar da hanzari. A gurguje ta kunna risho ta faɗa banɗaki bayan ta ɗora ruwan wanka. Jikinta a mugun mace ta fito daga banɗakin, daidai Gwadabe ya fito daga ɗakin Shafa zaije wankan tsarki. Shafar tana biye dashi da dukkan halamu tare zasu je suyi wankan. Lallai soyayya ta kai soyayya. Murmushi ta sakarma Gwadabe, murmushin daya kasance tamkar garwashi wajen ƙuna. Shigewa tayi ɗaki tana haki. A daddafe tayi ra'atanil fajir, ta ɗaura da sallar asuba. Ta jima sosai akan sallaya tana roƙon Allah ya sa mata salama a zuchiyarta game da wannan kishi mai kai mata mahallaka ya baro. Saida ta karanta Qur'ani suratul naba'i ta shafa adda'a sai taji zuchiyarta tayi wasai. Cikin sauƙin zuchiya ta shalla wanka, ta shiga gyaran ɗakinta cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala, a madadin kunna turaren wuta tunda bata da gawayi kuma yayi wuri ta aika gida a ɗebo mata saita kunna ɗan tsinke ta bishi da Room freshener na MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI mai ƙamshin oud Cikin ƙanƙanin lokaci gidan ya ɗauki saiti. Zama tayi a barandar data haɗa ƙofofin uku, tana iya hango masu gilmawa, suma suna iya hangota. Doya ta gutsura ta fereye kaɗan, ta ɗaura abun suyanta ta zuba mai ta soma suyan doya. Matar Sabitu ce ta fito tsakar gidan taci uban ƙananun kaya kanta babu ko ɗankwali kasancewarta mai gashi daidaiya, sai karairaye takeyi da ledar shara a hannunta ta gangara ƙasan gidan dan jefar da ledar shara a babban durom ɗin shara dake gefen bayan gidan tsakar gidan. Kai Hadiza ta jirjiza kawai. Doyarta ta soyu ta kwashe ta juye man a samira ta adanashi. Sai ta mayar da kaskon kan wuta ta fasa ƙwai biyu ta yanka albassa ta ɗan barbaɗa dunƙule ta soye ƙwanta gidan ya kaure da ƙamshi. Da ɗaya da ɗaya amaren gidan suketa fitowa domin ɗora abinda za'a durama ƴan hanji, dama dai kunsan Amare a gigice suke tashi da yinwa. Ruwan tea Hadiza ta haɗa dama tana da ruwan zafi a flaks ɗinta. Ta gama haɗa kayan karyawanta tsab ta kai ciki. Ta yafa mayafinta da ƙaton kaskonta me murfi ta fito tsakar gidan. Ta haɗu da matar Abdullahi da matar Jazuli, babu wanda ya kalleta itace dai ta gaishesu a wani wulaƙance suka amsata har suna shewa, ko ta mecece ohon musu dai. Ɓarayin su Yaya Tasi'u ta nufa. Da matar Yaya Jamilu ta soma cin karo Innar Khadija. Tana soya dankalin turawa a ƙofar kitchen ɗinta a gawayi. Tayi kaca_kaca da wajen, ɓawon dankalinma da ɓaron ƙwai duk ta zubar a ƙasa yara sun tattaka. "Me zan gani Amarya sassafe haka. Af na mance ashe zawara kwana uku akeyi mata ango ya koma ɗakin Amarya ko?" Ɗan murmusawa Hadiza tayi, inda sabo ta riga da tasan dama irin zaman da akeyi. Magana ta arziki bata haɗa kowa da kowa, face habaici da son gumama juna. "Hakane ango yana ɗakin Amarya. Nima gaushi nazo ku bani" Sai ta tuntsure da dariya tace. "Ga gaushi zo ki ɗiba kafin ku soma hura naku. Tunda me gidan maganin ƙarfin maza yake siyarwa" Ajjiye kaskon tayi, domin furucin Innar Khadija yayi mata zafi. Sun daɗe suna kushe sana'ar Gwadabe a cikin gida. Dan Amaryar Malam har yara take turawa da nera ɗari tace wai a bata maganin basir malam zata ba. "Bari in gaisa da Anty Badi'a tukunna sai inzo in ɗiba." Nan ta wuceta ta barta da zunɗenta ta baya. Tun daga kofar da zata sadaka da ɓarayin Anti Badi'a kake jiyo ƙamshi na tashi. Falonta tsab yasha gyara, ta shiga ta samu Sailuba na fesa Room freshener a labulayen ɗakin. Anty Badi'a data ci kwalliya da riga da sikert ɗan kanti wani mai tattara na zamanin tana gaban durowar da tv yake kai tana juna abun ƙona turaren wuta mai amfani da wuta ( electric burner wanda a lokacin batai yawa ba, sai gidan ƴan gayu ake iya ganinta) "Anty Hadiza, Mama ga Anty Hadiza " Cewar Sailuba kenan. Maman ta ɗago da dariya tace. "Uwargida sarautar mata ke ko me kike yi a nan sassafe kamar wacce tayi ɓatan kai?" Hadiza dake ta kallon falon kamar ta wanke makanta tace. "Ke dai Anty Bari. Kinga rushi nazo ɗiba inaso kafin in karya in kunna turaren wuta" Sai Anty Badi'a tayi Dariya tace. "Ina zuwa. Sailuba ki zuba mata farfesun kan ragonnan a ƙaramar kula maza" Ta shige ɗaki sai gata da sabuwar ( electric burner) a kwalinta ta miƙa mata dama guda biyu ta siyo tafiyarsu Umara ita da mijinta. "Ga wannan aita ƙona turare lafiya." Hadiza ta amsa da murnarta taima Anty Badi'a godiya mai yawa. "Na ganki da leshi kina wayayya. Ai leshi kwalliyar dare ce, ko rana. Da safe ai ƙananan kaya ya kamata ki mayar su zama ababen sawarki. Karfa ki ba damu yarinya ƙarama ta ciri kambu" Hadiza ta zaro idanunta waje tace. "Nifa Anty ƙananan kaya guda ɗaya jol gareni. Wata rigace doguwa mai hannu ɗaya. Itama ƙawatace ta kawo mun. Ina dai da rigunan bacci" Miƙewa Anty Badi'a tayi tace. "Jira" Bata jima ba sai gata da leda ta miƙo ma Hadiza. "Kije maza ki sake kayan jikinki ki sa wannan. Zuwa anjima Sailuba zata zo ta kira mun ke. Akwai Hajiyar da nake siyayyar ƙananun kaya a hannunta kayanta suna da kyau Dubai take siyosu. To anjima dama zata kawo mun kaya, da ƴan sabulan gyaran fata." Cikin murna Hadiza ta fito tana shima Anty Badi'a da albarka. Koda ta fito bata ga Innar Khadija ba, ta ɗebi gaushinta ta wuce. Tana kunna turaren wuta ta shige ɗaki ta buɗe ledar da Anty Badi'a ta bata. Riga da sikert ne irin na jikinta sak kalace ta bambanta. Na jikin Anty Badi'a siket ɗin mai ruwan gorrone, sai rigar mai ruwan madara da kwala a wuyan rigar. Ita kuma Hadiza nata siket ɗin kalan jinin karene maron sai rigar mai ruwan madara. Ta saka kayannan yayi ɗas a jikinta rigar ta ɗan matseta dan tafi Anty Badi'a cikar ƙirji. Tana gyara gashi ta jiyo sallamar Shafa a falo. Shi kuma gogan naka masu abu da abunsu sai ya kutso kai ya shigo cikin uwar ɗakin. Ƙur yayi mata da idanunshi yana mata wani mahaukacin kallo mai ɗauke da guguwar sha'awa da burgewa a ciki. Manna ƙirjinshi yayi a nata ƙirjin, yayi lub a jikinta yana shaƙar ƙamshin dake saurin tayar mishi da jarabarshi. Ajjiyar zuchiya Hadiza ta sauke. Gwadabe ya ɗago idanunshi da suka sauya kala yace. "Wallahi kinyi kyau sosai. Kayannan ya amshi jikinki da fatarki ƴar duma_dumata" Murmusawa tayi wani farin ciki ya baibaye zuchiyarta. "Nagode ango mijin Amarya. Naga sai sheƙin angwanci kake yi." Murmushi yayi mata dan yaji sautin kishi a muryar tata. "Shafa tana falo kizo muci abinci." Da sauri ta kalleshi tace. "Abinci kuma, a ina za'aci abincin ba'a ɗakin Shafa kake ba?" Dariya yayi mata. "Abincinne nace ta ɗakko muzo muci a nan ɗin. Hakan nake so mu dinga yi, sabida zai samar mana nutsuwa da fahimtar juna. Wacce bata da kwana ma zata samu damar zantawa da mijinta. Muje ko?" "Amman Yaya Gwadabe" "Shishshsh... Bana son kice komai, kizo muje" Ba dan ran Hadiza yaso ba dai. Tayo jigum har Gwadabe ya fice tana tsaya tana tunanin ta ina wannan lamarin zai soma. Yama za'ace wannan tsarine me kyau. Me yasa wacce take da miji ba zata zauna ita kaɗai da mijinta ta samu nutsuwa su ciyar da juna abinci a baki cikin shagwaɓa da soyayya ba? Ɗan guntun tsaki ta yi kana ta fito rannan nata a mugun ɓace. Ɗakin ya cika dam da hayaƙin turaren wuta ko ina yanata bulbula ƙamshi masha Allah. A gefe guda ta zauna tana fuskantarsu tare da ƙarema tiran abincin Shafa kallo. Itama Shafar ita take kallo tun futowar tata. Sanye take cikin riga da zane na atampa ɗinkin wasila. "Yaya ina kwana, an tashi lafiya?" Kallon Shafa tayi sai ta saki fara'a a zahiri, a baɗini kuma ji tayi kibiyar kishin Shafa ta soki murfin ruhinta. Gani tayi a idanunta shafa tayi kyau kaalar atampar ta amshi fatarta, sai kishi ya bijiro mata. Ta bangaren Shafa ma fitowar Hadiza saida ya faɗar mata da gaba, take ta raina kwalliyar data kashe minti talatin tanayi. Kuma ƙamshi Hadiza ya goge tarihin turaren akwati data fesa ta fesama Gwadabe ma. (Ire_iren wannan ke hana zaman lafiya a tsakankanin kishiyoyi. Shi yasa akeso mace ta yarda iya wuya tafi kishiyarta. In tasa hakan a ranta ta huta da kaso hamsin. Muddin duk abinda zai faru kina hango cewar an fiki, to akwai matsala. Anya gidan Gwadabe zai zauna lafiya kamar yadda yake tunani kuwa. Mu dai je zuwa mahaukaci ya hau kura) "Lafiya lau Amarya. Mai gida takobin yaƙi ina fatan kabi da'ita a hankali kaga yarinyace kuma kai ɗin baka da dama" Ta ƙarashe zancan da wata mayaudariyar dariya mai sukurkuta kan mai gida. Sai murmushi yayi dan shingin kaɗanma ya ƙware da tean da Shafa ta zuba mishi yana kurɓa. Dariya kawai yayi, ita kuma Shafa kunya ta mamaye illahirin jikinta. Taliyar Hausa ce da miyar stew ta zuba musu ta caɓa miyar akai sai ruwan bunu mai citta. A plate ɗaya ta zuba ta saka cokula uku. Murmushi Hadiza tayi tace. "Ayya ai da baki zuba dani ba. Kinga abincin karyawata na riga dana kammala." Kallonta Gwadabe yayi bayan ya kai lomar taliyar bakinshi. "To ba sai mu haɗu muci duka ba Hadiza. Ita Shafa ai ba zata ji daɗi ba in baki taɓa abincinta ba." Ɗan gajeren murmushi tayi tace. "Shafa zuba mini shayin in sa albarka. Doyar na tashi ina sha'awar ci, dan da zazzaɓi ma na tashi" Kalmar zazzaɓi ne yasa Gwadabe ya sarara baice da Hadiza uffan ba, duk da yasan lafiyarta ƙalau abincinne ba zata ci dasu ba kamar yadda tayi rannan. Doya da farfesun ta raba biyu ta ajjiye musu rabi, ta soma cin nata. Ɗakin yayi tsit baka jin motsin komai saina lokula da tauna. Su ukun duka ko wanne da abinda ke ƙunshe a ranshi. "Hadiza kece babba ina mai ƙara baki haƙuri dan Allah ku daure ku wanzar da farin ciki a wannan xamantakewar. Kunga ni a zaman da nayi da uwar ƴaƴana bamu taɓa samun saɓanin da har za'ace mun kwana muna rikici, ko gaba da sauransu ba. To ina fatan kuma zan sameku kamar Iyabo, koma fiye da ita dan a zahirin gaskiya Iyabo mutum ce guda da ɓari. Ina fatan mu zauna Lafiya " Take kishin Iyabo ya turniƙe Hadiza ta yanda ya kusan rufe mata idanunta tayi ɓaranɓarama. Allah ta ambata a zuchiyarta taja bakinta ta yi shiru. Abincin dake gabanta ma rufewa tayi dan sai taji bakinta na wani irin ɗaci. A cikin zuchiyarta tace. "Niko zanso ganin wannan Iyabo ido da ido inga me ta mallaka wanda yayi tsaye cak a zuchiyar Gwadabe da har mu yake ma ishara da muyi koyi da ita wajen kyautata xamanmu a tsakaninmu dashi " "Bakice komai ba ke Hadiza " Gwadabe ya katse mata zaren tunaninta. "Allah ya bamu ikon haɗe kanmu mu baka nutsuwa" A haka dai suka kammala cin abincin Shafa ta soma kwashewa. "Meye ya ɓata miki ranki haka Hadiza. Wai me yasa kike yin hakane Hadiza ta? Haba gimbiyar mata tauraruwar zuchiyar Gwadabe " Harara ta watso mishi tace. "Iyabo tana numfashi na zama tauraruwar zuchiyarka?" Dariya yayi kafin yace wani abu Shafa ta shigo. Dole shima ya miƙe yai mata sallama ta bisu da idanunta sai ga hawaye sirara sun zuraro mata. Da sauri ta share hawayen nata ta miƙe ta soma gyara wajen da akaci abincin, duk da dai ba datti a wajen. Sallamar Ine Hadiza ta jiyo daga ƙofar ɗakinta. "Ah su Ine manya kune a gidan sassafe?" Zama Ine tayi tace. "Ke dai bari yanzu na shiga cikin gida na tarar da Malam na rikici da Baba Suwaiba, da Amaryar Malam. A taƙaice a kan idanuna duk Malam ya koresu sun fice da akwatunansu. Gaskiya ban taɓa ganin ɓacin ran Malam irin na yau ba." Daɓas Hadiza ta zauna a kujera. "Malam ya koresu fa kika ce, to me suka yi haka?" "Tabb wallahi ban sani ba, kinsan Baba ba faɗamun zata yi ba kona tambaya. Ni ban tambaya ba. Babace tace in koma gida kawai, shine nace baro in shigo mu gaisa zan shiga wajen Anty Badi'a ma" Hadiza tayo jigum kana tace.." "Zanga sanda gidanmu zai daidaita. Kishine ko wacce ya cika mata ranta fal. Amaryar Malam na jima ina ɗauke da cikinta ba dan tana cin albarkacin mahaifina take aureba da tuni ta gane kuranta. Sabida tana da fitina da yawa fiye da sauran iyayen namu." Nan dai suka ɗan taɓa hirarsu Ine tai mata sallama ta tafi. Sai wajajen azahar Sai ga Sailuba tazo kiranta. Wayarta ta ɗaga ta kira Gwadabe ringing biyu ya ɗaga. "Gimbiya lafiya dai ko?" Murmushi tayi tace "Lafiya lau. Dama Anty Badi'a ce tace tana son ganina shine nace bari in sanar maka" Sai da yayi murmushi yace. "Masha Allah kije ba damuwa. Ni bana gidanma muna wajen Malam, an ɗan samu kacaniyane a cikin gidan. Sai dai inna dawo zakiji komai" "To Shikenan saika dawo ɗin." Wayarta ta kashe suka fito ita da Sailuba. Su Yaya Jazuli da su Nazifi suna ɓarayin Yaya jamilu. Suma zancan korar mahaifiyarsu da Malam yayi a gidan suke yi. Karaf a kunnen Hadiza Nazifi yana cewa. "Dole zamu je mu dawo da uwarmu babu inda zata je, tunda ta haifemu muna da gado a gidan" Hadiza ta kalleshi shima ya kalleta yana muzurai. "Dena kallona dan ta abu kazan..." Ya danno wani zagi ya dannawa Hadiza tare da ɗorawa da cewa. "Ku gaku ƴaƴan so, yaran mowa shafaffu da mai. To wallahi wannan abun masifa da bala,i kawai zai haifar dam mahaifiyarmu ba zata koru ba" In kun tanka Hadiza ta tanka. Inda sabo ta saba da jin waɗannan zagi da waɗannan furuci na cewar sune ƴaƴan so a idanun Malam. Haka zalika dukkan abinda ya faru a wannan gida nasu gani akeyi dasa hannu Baba Fhatsima da Yaya Tasi'u da suke ganin kamar suke juya Malam. Hadiza ta shiga tunanin yanzu haka suma in suka ƙi samun zaman lafiya a tsakaninsu yaransu zasu taso a cikin ƙiyayyar jininsu? Wai to wake da Matsala ne mazan dake auro matam su haɗe su. Ko kuma matan da aka aurone masu matsalar? Ita dai tasan matsalarta ɗaya kishine, kuma kishi shine matattakalar data rusa ahalin gidansu da duk gidajen da aka kasa samun daidaito da fahimtar juna kuma ba mace ɗaya bace a cikin gidan. Duk kishi shine sababin dake sa uba ya tsani ƴaƴan cikinshi, uwa taji kamar ta kashe ɗan da kishiyarta ta haifa, kishiya da kishiya su kasa samun zaman lafiya. Gida ya zama gidan rikici da hayaniya kullum. Wannan lallai babbar matsalace da Hadiza take ganin bai kamata ta bari sheɗan yaci galaba a kanta ba. Take zuchiyarta ta sassauto mata dangane da zafin kishin Shafa. Duk da bata da burin yin zaman doya da manja da Shafa. Amman ta ɗaura ɗamarar saita zama tauraruwa sarauniya a birnin zuchiyar Gwadabe ta yanda zata ture har matsayin da Iyabo take dashi. Da wannan tunani ta shiga falon Anty Badi'a. Suna zaune a ƙasan kafet an barbaza kayayyakin mata na ado da kwalliya kyawawan gaske Anty Badi'a sai ɗagawa take yi. Hadda manyan zannuwan gado ƴan kwali irinna saudiyya ɗinnan masu laushin gaske. "Kinga yadda kayannan suka amsheki kuwa Hadiza? Ga wasu samfurin masu wando, da gajeren siket an kakkawa zo zauna." Cewar Anty Badi'a. Zama Hadiza tayi da hanzari suka soma ɗaɗɗaga kayayyaki harda wasu rigunan bacci na garari . "Kinga zaɓi kaya Hadiza. Ba'a bori da sanyin jiki. Kinga waɗannan dana zaɓar mana ni dake, duba kiga kalolin sunyi" Anty Badi'a ta miƙo mata kayayyakin ta soma waresu tana gani, dogayen ruguna, da riga da wandone, sai kuma mai gajeren siket wanda zaka saka daga kai sai mijinka. Kaya dai kusan guda takwas_takwas harda zanin gado na kwali mai ɗawisu irin na da. Hadiza rabin kuɗin kayannan ta biya, Anty Badi'a ta biya mata kuɗin rabin. Ta sake yin mata kwalimar nata ƙananun kaya. Ta bata wasu surruka masu ƙarfi tace ta riƙesu tayi amfani dasu zata ci ribar zaman Aure. "Fatanmu shine mutuwa itace zata rabaki da mijinki. Kinga maza kullum su babban birinsu shine mace ta zama musu tamkar hawainiya wajen caccanja salo_salo na komai nata ta yanda zamanku bazai zama ya gundureku ba. Ki tabbatar a ranar dazai bar ɗakinki kin mishi abinda zaiji yana ɗoki da mararin sake shigowar girkinku. Ki riƙe talaucinshi kuita mishi adda'a Allah zai buɗa mishi Gwadabe yana da zafin nema ba malalaci bane muna mishi fatan nasara. A ido haka Shafa bata da wani matsala kiyi ƙoƙarin janyo ta a jika, karki bari wasu daga cikin gidan su janye miki ita da hakanne gulme_gulme ke ratsowa. Hadiza ai Baba ya kamata ta zame miki allon kwaikwayo. Dan har gobe kinga yadda ruwa yake maganin dauɗa. Anty Badi'a ta jima tana bawa Hadiza surrukan da zasu tallafi zamantakewarsu daga ƙarshe sukai sallama Hadiza ta koma ɓarayinta. Gaga gaga haka rayuwa taci gaba da matsawa, duk safiya da irin shiga da Hadiza take yi na alfarma, ga ƙamshi. Itama fa Shafa bawai a baya aka barta ba itama tana yin nata salon kwalliyar, amman ita tafi ganewa atampa, leshi sai dogayen riguna ƴan kanti. Itama suta riƙe a matsayin makaminta. Ko wacce cikinsu rigegeniyar take yi wajen ganin ta zama ta gaban goshi. Rayuwar gidan babu daɗi domin kuwa wasu basa ko ga miciji da wasu. Ko wanne ƴan ɗaki isu_isu da matansu suke mu'amala, gaisuwa wannan bata shiga tsakani. Shi yasa tsakaninsu Hadiza da matan su Auwala ne kawai suke mu'amalarsu a tsakaninsu, sai Yaya Tasi'u daya zame musu garkuwa. Ko wacce in zata fito bata da aiki sai waƙe da habaice_habaice. Sai gasa da hassada ta shigo cikin lamarin. Daga masu suyan kifi, sai masu suyan nama, ko kaza. Ga gasar sutura da kwalliyar safe data yamma dan tarbar miji." Ta bangaren gidan Malam kuwa rikicine ya ɓalle ƙaramar maganace take son zama babba. Iyayen matanshi daya tura gida sunyi jelen har sun haƙura. Amsa ɗaya malam yake faɗa musu itace "Su je su huta a gidajen iyayensu. Nima inaso in huta" Yaran Baba Suwaiba suka haɗe kansu suka samu Malam akan batun gyatumarsu. Suma Malam ya fatattakesu da zancan. Bayan kwana uku suka je suka dawo da Babarsu gidan. Ranar sunga tsiya. MRS BUKHARI Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801 Hello Maamas.. Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa. Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi😆 Muna da; Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su. Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata😍 Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci 08067145801 Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri👏🏼kamar yarda muka Saba duk sallah munayin adashin kayan sallah Dana kayan kitchen to wannan lokacin ma lokaci yayi @ zee Musa collection taxo muku da hanya Mai sauki domin ga number 📞📞📞08029882667 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata 💃🏼💃🏼💃🏼🤣 idan matsalarki rashin sabbin plates 🍽️idan axumi yaxo 🍽️ to ansamu hanyar maganin wanan matsalar idan kina son siyan atamfane da lace Amma bakida kudi a lokaci daya to duk Dama ta samu Zaki iya shiga wannan dashi namu mu Aiko muki da kayanki ako Ina kikyee da yarda Allah Akwai 1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k 💃🏼 Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa 💃🏼💃🏼💃🏼hardakyee domin akwai tsarin zubi duk karshen wata iya yarda Zaki iya idan lokacin daukarki yayi ki Fadi duk abunda kikyeeso atura muki ko menene har supplement domin gyaran jikin domin ba iya Kaya muka tsaya ba wasu abubuwan ma sai ka shiga group Dina zakasha kallon sabbin abubuwa masu kyau da Kuma sauki Akwai kayan Yara yankanti Akwai takalman da jakunkuna da mayafai Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce 💃🏼💃🏼👍🏻🥰 ga number din da zaa iya damuna 💃🏼💃🏼🤣📞📞 08029882667 *Ina kuke mata ƴan ƙwalisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haɗaɗɗun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.* *Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu* 07082649563 whats app number kira 07036028230*INA MASU SAN SIYAN KAYAN ƘAMSHINA? NESA TAZO KUSA ZAN TURO DA KAYA KANO DAGA KANO ZA'A TURA MIKI DA KAYANKI DUK GARIN DA KIKE, IN A KANO KIKE KAYANKI HAR GIDA ZAI ISO MIKI IN SHA ALLAH. KAYAN ZASU ZAUNA A HANNUN ANTY ZEE MUSA COLLECTION DA IZININ ALLAH KAMAR YADDA AKA SABA. IN KINA BUƘATA KIYI MAGANA A HAƊO DA NAKI KAYAN HAJIYA* *ƳAN PROMO SUMA SU SOMA TURO DA KUƊIN PROMO ƊINSU. 10k NE ABU UKUNE A CIKI. IYAKAR NA MUTUM HAMSIN ZAN HAƊA MASU SO SUYI MAGANA KARKU BARI WANNAN PROMO YA WUCEKU* *WAƊANDA SUKA SAN KAYAN PROMO NA NASAN BABU WASA. IYAKAR MASOYANA NE KAWAI PROMO DINNAN BAZAN SIYARMA DA NA WAJEN GROUP BA. KAYAN 20K NE NA BAR MUKU A 10k DOMUN KU DA BAKU TAƁA AMFANI DA KAYANA BA KU JARABA* *WAƊANDA KUƊAƊENSU YAKE HANNUNA DUK ZAN SALLAMEKU SANNAN AKWAI KYAUTA DA ZAKU SAMU IN SHA ALLAH.* *WAƊANDA BASU TAƁA SIYAN KAYAN ƘAMSHINA BA SUMA AKWAI KYAUTA TA MUSAMMAN DA ZAN BAKU IN SHA ALLAH.* NAMA YA DAHU.. ROMO ƊANYE GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI 20 "Wallahi Suwaiba ba zata shigarmun gidana ba, tunda ba da kudinku na gina gidan ba. Ki koma gidanku ki huta, kinganni hutu nake buƙata ni kam" Cikin marairaicewa Baba Suwaiba tace. "Haba Malam ai in adalcine sai ka sallami matan naka duka, bamu ka waremu ba su ka barsu ba. Sannan Malam wanne irin haƙurine daga gida ban turo an baka ba ne? Sagiru kasa baki" Ta dubi Sagiru halamar agajinshi take nema. Dan dama yafi kowa rashin kunya a cikin gidan. "Baba muje ki zauna a ɓarayinmu, mun riga mun ɗakkoki daga gidanku ai ba kya koma ba. Muje kinji ki dena damun kanki" Ya kinkimi akwatinta ya kaita wajen Amaryarshi yace ta zauna na wani lokacin. Haka kuwa Baba Suwaiba taci gaba da zaman takura tana kwana a falo akan doguwar kujera. Kwananta biyu ƴarta ƙanwar Sagirun Aisha tazo ta ganta, ta tattageta zuwa nata gidan tunda su suna da estira ɗakin da zata zauna ita kaɗai. Amaryar Malam kuwa tana gidansu zaman gidan babu daɗi, gashi mahaifinta yace shi ya gaji bazai sake zuwa ba Malam hakuri ba. Wannan lamarin ya sake farraƙa kan gidan Malam. Bayanin da Baba Fhatsima take ta yi mishi kenan babu dare babu rana kan hakan ba ɗa mai idanu zai haifar ba. Shi kuma yace ta zuba mishi idanu data matsa sai cewa yayi. "Fhatsima in kika matsamun akan batun su Suwaiba, to zaki sa in sallamesu gabaki ɗaya su fice mun a gida. In yaransu zasu bisu duk su haɗa dasu. Ina amfanin yaran da basa dajarta ubansu ne?" Dole haka Baba Fhatsima ta tsuke bakinta tayi shiru. Da Baba Asshi da yaranta sai suka shafama kansu ruwa, dan basa fatan uwarsu ta bar ɗakinta azo ana roƙon Malam yana botsarewa. Wannan kenan" Yau monday tushen aiki. Ayau Angwaye zasu koma bakin aikinsu kasancewar yau satinsu guda tim da tarewa a ɗakunansu. Wanda yayi dai_dai da kwanan Gwadabe huɗu a ɗakin Shafa. Tun asubar fari Gwadabe ya hura huta ya ɗaura ƙatuwar tukunyar maganinshi, yana dawowa Sallah ya sauketa. Shafa ta juye mishi ruwan wanka, shi yana shirin fita kasuwa ita kuma ya kwatanta mata yadda zata ƙulla mishi maganin nashi. Tana girkin safe tana ƙullin magani. Gwadabe shi kuma ya shirya tsab cikin kayan nema ya fito ya kama ɗaurin magani. Ita kuma Shafa ta samu damar kammala haɗa kayan karin kumallo a babban tire, ta shiga ban ɗaki ta watsa ruwa. Cikin kanƙanin lokaci ta shirya cikin doguwar rigar shadda mai ruwan ƙasa tasha surfana. Tana fitowa Gwadabe ya kalleta yace. "Kinyi maƙurar kyau Shafa. Ki kai abincin ɗakin Hadiza nima ganinan" "Godiya nake yi mijina na kaina" Murmushi yayi mata yana son sanyin halin Shafa sosai. Tiran ta ɗauka ta shige ɗakin Hadiza, bayan matar Sabitu ta ja dogon tsakinta. "Gwadabe kayi da jiki bakwai harta gota, Mammada fa harya fice yana jiranmu a ƙofar gida, kai kuma naga sai yanzu ma zaka karya" Cewar Auwala daya fito cikin shirin fita kasuwa" "Bari kawai in musu sallama sai in fito mu tafi. Ko ƴar tsala naci acan in munje." Miƙewa Gwadabe yayi tsaye da sauri. Bokitin maganin ya kinkimo ya fito dashi tsakar gidan, ya ajjiye tsumman da yake gammo dashi, ya samesu a ɗakin Hadiza. Itama Hadiza taci ado yau da Atampa riga da zani, jakarta da mayafinta yana gefenta itama hutun da makarantar su ta bata ya ƙare yau. "Barka da Safiya yallaɓai, lafiya ka tsaya a kanmu sai binmu da kallo kake yi?" Cewar Hadiza da take magana a ɗan shagwaɓe. Yana matuƙar jin daɗin shwagwaɓar Hadiza da yadda take taimakonshi akan shimfiɗa wajen tayashi cimma manufa. Saɓanin Shafa da take kwanciya kamar ruwa sai inda aka juyata" "Kunyi kyaune. Nake mamakin ni Gwadabe mahaƙin gwal, mai saida maganin basir nine da mata fella_fella haka? Allah nagode maka. Kuyi haƙuri abincinnan bazai ciyu ba. Su Auwala ni suke jira, saina dawo zanci abincin acan. Hadiza yau zaki koma bakin aikinki kema ko?" "E hakane. Ni kaina jiranka nake yi dama ka shigo in muku sallama, inna tsaya yin breakfast a gida zanyi latti. To acan nake karyawa ina tafiya da filas ɗin tea da abinci" "To Shikenan tunda Hakane. Na soke karyawar safen. In yaso da daddare ma dinga haɗuwa, ni na tafi. Shafa ki yi haquri ki koma ɗakinki da abincin" Sam Shafa bata ji daɗi ba. Tana lure dama Hadiza bata son cin abincinta, kuma ita ta duba ta hanga bata ga ta inda Hadiza ta fita tsafta ba. Ba dai tasan irin daɗin girkinta ba wannan, tana jiran ranar girkintane taci taji" Tiran abincin ta ɗauka. "To Yaya sai kin dawo" Tasa kai ta fice. Tana fita Gwadabe ya jawo Hadiza dake tsaye jikinshi, ya cusa kanshi a kirjinta yana ajjiyar zuchiya. "Uwargida a matse nake dake fa sosai. Ina mararin juyowar girki bazan ɓoye miki ba" Idanu ya lumshe yana hasaso daren ƙarshe da yayi a ɗakin Hadizan. Murmushi tayi mishi tace. "Kamar yaune lokaci zai zagayo, harma ya wuce. Haka zakaita zagaye har abada, tunda burinmu mu dauwama tare da kai har abada" Ba shiri dole ya saketa ya fice, ta biyo bayanshi suna dariya. Gwadabe ya suri bokitin maganinshi ya fita. Auwalane ya ɗaura mishi aka suka nufi hanya, Allah cikin ikonshi kafin su isa inda zasu hau abun hawa Gwadabe yana taɓa ciniki babu laifi. Acan inda ake aikin haƙon zinare kuma tas maganinshi yake ƙarewa sakamakon maganinshi yana da kyau, kuma masu saye sun shaida yana musu aiki. Gashi yana gaba_gaba wajen haƙon zinare, Gwadabe namijine mai zafin nema da zafin nema babu wasa a lamarin aikinshi. Haka rayuwar dai taita garawa yau mun wayi gari Gwadabe ya gama kwananshi na ƙarshe a ɗakin Shafa, ya fita da safe inya dawo a ɗakin Hadiza zai ya da zangonshi. Sannan yana fitowa Yaya Tasi'u ya bashi takaddar samun aikin Shafa, a wani asibiti zata dinga ba da kati. Gwadabe yayi murna sosai kuma ya yaba da ƙoƙari da kulawar Yaya Tasi'u gaya. Mutuniyarku Hadiza yau wayar garin tayi tamkar anyi mata bushara da gidan aljanna dan daɗi. Tana cikin farin ciki ta tafi makaranta. Hatta ƙawayenta malamai sun gano farin cikin da take ciki. Sadiya uwar zolaya, bayan Hadiza ta fito daga aji ta dawo ofishin malamai dan tanaso ta karya kafin lokacin komawarta wani ajin yayi tace. "Waini Hadiza ko Gwadabe yayi muku wata gagarumar kyautace yau ɗinnan? Hatta kwalliyar da kika caɓa naga ta dabance, harfa taku kika canja." Dariya gabaki ɗaya matan cikin ofishin suka saka. Hadiza saida ta tura wainar ƙwai bakinta kana tace. "Sharri dai da sa ido Chima in ba haka ba wacce canja tafiya nikam zanyi? Kawai dai yau nice da girki shine naketa nishaɗi. Kuma inata tunanin wanne irin abinci zan tari Oga dashi, tunda mu kai aure baici abincina ba, in banda farar shinkafa dana dafa muka ci da Miyar da Balaraba ƴar ƙanwar Baba ta soya. To Ku bani shawarar abinda zan girka, da irin wankan da zan fella Sadiya kune masu kishiya, bani labarin yadda kike tashin kan abokiyar zamanki ran girkinku?" Wata dariyar mugunta Sadiya ta shiga yi har tana tuntsurawa. "Wallahi har kin tuna mun da Safara'u. Ranar girkina sam bata da sukuni, kalar tausayi take zama. Gashi Sanusi shi ƙa'idarshi a turakarshi muke zuwa cin abinci. Gaskiya kusan kullum da jan idanu take fita in ranar girkinane" Hadiza tayi shewa tace. "Shegiya ƙawata. Bani sirrin mana nima in ƙara da nawa. Kinsan Allah inason mijina sosai, kuma in na kalli Shafa a kullum sai inji kamar ma in shaƙeta uban kowa ya huta. A kallon da nayi mata lokacin biki, banyi tunanin zafin kishina zai iya sauka a kanta ba, danni na raina yanayinta kuma nasan ƴar ƙauyece duk da tayi karatu. Ashe wallahi kallon tsoro nayi mata itama akwai kaya. In ta shawo wankannan suka shigo mun ita da Gwadabe kuma naga hankalinshi a kanta. Kinsan Allah kamar in zazzagama kaina fetur in ƙone haka nakeji dan kishi." Dariya suka kwashe dashi. Barira tace. "Ni uwargidanmu batta da son girma amman bata da damuwa. Amman Nabila itace take neman ɗauramun hawan jini a baya. Sai da Sadiya ta bani maganin damuwar da Nabila ta so ɗauramun. Shawarwarine nagartattun da dabarun yadda zaki zama wata ta daban a zuchiyar oga, da kissar danne kishi. Kinga da ɗan abu kaɗan Nabila zata yi, kawai sai inji kishi kinsan Allah bana sanin sanda nake lailayon mata uwar ashariya. Kinga ina girma a wagga lamari?" Dariya suka kwashe dashi. Ƙararrawa aka buga dole Hadiza na jin daɗi ta tafi aji dan ba yara darasi. Data dawo suka ɗaura, Sadiya ta zauna ta karanto mata abubbuwa masu girman gaske ( Sannu a hankali zaku jisu a aikace cikin labarin) Waɗannan maganganu su suka sake buɗe kan Hadiza tayo farin ciki gaya. Ana tashi ta wuce wata ƴar ƙaramar kasuwa dan yin cefanen naman rago ta siyo, sai bushasshen kifi, da cefanen tumaturi da su tattasai, attaruhu. Albasa an kaita dashi kusan rabin bihu ma. Sai kankana kwallo daya da lemun tsami manya na nera hamsin. A gajiye ta shigo gidan, babu kowa a tsakar gidan ɗakinta ta buɗe ta shiga. Ta ɗan kwanta ta huta bacci ya ɗebeta zuwa la'asar. Da sauri ta miƙe ta fito, daidai Shafa ta fito daga banɗakinta da halamun alwala ta ɗauro" "La Yaya yaushe kika dawo?" "Na dawo bayan azahar, nayi tunanin ko bacci kikeyi shi yasa ma ban tasheki ba ni kam. Kinga bacci nayi yanzu na farka" Shafa tace. "Ai kuwa bacci nima na tashi yanzu. Dan ɗazu naso yin baccin amman an ɗanyi rikici a gidan akan shanya abinda ya hanani baccin kenan" Haɓa Hadiza ta riƙe. "Akan shanya kuma, to dawa dawa su kai faɗan?" Shafa tace. "To matar wancan ɗakin na gaba can, da matar ɗakin dake kallo nakine. Sunyi faɗa sosai harda fashe bokatai fa" Baki Hadiza ta taɓe. "To Allah ya kyauta, bari inyi sallah " Tayi wucewarta banɗaki, Shafa itama ta shige nata ɗakin. Tana idar da Sallah ta sauya kayan jikinta zuwa wata ƴar doguwar riga mai sauƙi haka, ta fito domin soma girki. Matan gidanma kaf ɗinsu suna kitchen anata ɓuruntu. Gida ya kaure da ƙamshi kifine, kazane kowa dai da abinda yake girkawa. Sanwar miya Hadiza ta tsayar. Tana tsintar waken da zata zuba a miyar. Baba Suwaiba ta fito tsakar gidan tana sababin danme za'a hana surukarta shanya. "Ke Fatima ki fito fitsararriya kwashasshiya fito inji me kika taka" A madadin ita ta fito sai Sabitun ya fito da kanshi. Rashin kunya yayi mata, dama basa ganin kowa da gashi a gidan. Nanfa rikici ya ɓalle rikicin da sai da Malam da Baba Fhatsima suka yo tattakin shigowa. Daidai Baba Suwaiba tayi ɗamara ta nufi Sabitu da duka. Malam "Yayi kyau Suwaiba Nagode gaya. Ku kuma duk ku watse ko wacce ta shige ɗakinta. Gobe da safe daku da mazajen naku ina nemanku a gida bakwai na safe. Kai kuma Sabitu sannu da Uwar taka kake sa'insa sabida ɗiban albarka ko?" Iyakar abinda Malam yace kenan ya juya ya fice. Idanu Hadiza da Baba Fhatsima suka haɗa. Ƙunci da damuwa ƙarara a shimfiɗe a fuskar Baba Fhatsima. Kai ta gyaɗa ta bi bayan mijinta. Suna fitowa Baba Suwaiba ta biyo bayansu. Tsautsayi malam bahaushe yace baya wuce ranarshi. Kuma shi dana sani ƙeyace. Malam na ganin fitowar Suwaiba yace. "Na sakeki Suwaiba. Aurena dake ya ƙare, na gaji da baƙin ciki da takaicin da kuke ɗauramun ina shanyewa tsawon shekaru. Zuchiyata tarwatsewa kukeso tayi, ko faɗuwa kuke so inyi in mutu in bar baya da ƙura. To ta faru ta ƙare kije dan kanki." Baba Fhatsima ta dafe ƙirjinta. Baba Suwaiba kuma ta fashe da ihu harda kururuwa. Malam ya tafi ya barsu su biyun a tsaye yana tafe dafe da kanshi da yake jin kamar zai tarwatse. "Ki ƙarama bokanki kuɗi Fhatsima burinki ya idasa cika. A baya har hauka kika sa nayi na fito tsirara. A yanzu kinsa Malam ya sakeni ni Suwaiba. Ki rubuta ki ajjiye akwai ranar ɗaukar fansa tana tafe duk daren daɗewa ni Suwaiba saina saki zubar da hawaye." Cikin kuka take maganar. Murmushi Kawai Baba Fhatsima tayi tace. "Allah ya kyauta. Nasha tabara na sha yasin" "Ki ƙara da amanan rasulu. Fhatsima sai naga bayanki dake da yaranki duka, dani kike zancan" Har Baba Fhatsima ta ƙule Baba Suwaiba na zage_zage. Wannan lamarin ya rura wutar hatsaniya mai girma hatsaniyar da a tarihin rayuwar iyalin malam ba'a taɓa yin irinshi ba. Dan abun yakai harda faɗa da makami a tsakanin yaran Baba Suwaiba da su Auwala da suke kare uwarsu. Baba Fhatsima sai kulleta akayi ita da Malam a turaka. Yaya Tasi'u kuma ganin abun ya wuce gona da iri sai ya kira ƴan sanda aka fita da yaran Baba Suwaiba zuwa police station domin yima tubkar hanci. Malam yana goye da hannunshi a bayanshi sai kai kawo yake yi harda hawaye a idanunshi. Abun a tausayane ace dattijon magidanci yana hawaye ku kanku kunsan abun yakai intaha. Tunaninshi yake mayarwa baya a lokacin da suke rayuwarsu ta talauci da tsantsar soyayya shi da Fhatsima. Fhatsima tayi mishi son da harya koma ga Allah ma bazai samu macen da zata soshi rabin haka ba. Gashi a sakamakon giyar jini a jika da giyar kuɗin da bai taka kara ya karyaba ya ɗebo ma kanshi kara da kiyashi ɗaukar marar sani. Yau shine aka tura a ɗaki ƴaƴan cikinshi na fito na fito dashi kan uwarsu. Fhatsimar daya raina a baya ita da ƴaƴanta a yanzu sune garkuwarshi. Madallah da mace tagari, madallah da uwa tagari. A daren Malam ciwonshi ya tashi bil haƙƙi gaga_gaga aka wuce dashi asibiti. Hankulan kab ƴan gidan a tashe yake gaya. Dan ɗaiɗaiku daga cikin ƴaƴanshi masu mishi fatan mutuwane kawai sukai baccinsu harda minshari. Masu son rayuwar malam sune suka kasa rintsawa har zuwa wayewar gari. IYABO:. Satinmu uku a asibiti. Sai godiyar Allah domin jikin Dada ana samun haske sosai, har hira muna yi da'ita. Da safe da Yaya Hamma ya shigo ya miƙo mun Madara mai zafi a cikin gora. Sai Dada ta dubemu tace. "Hamma ko bayan babu raina Jabu itace matarka. Nayi imanin a hannunka zata samu nutsuwar data rasa a baya. Ina mata fatan samun miji tamkar mahaifinta Adetoye. Mutumne mai yakana wanda yasan darajar mace." Yaya Hamma yace. "Dada ai Jabu ƙanwatace ko bani na aureta ba sai inda ƙarfina ya ƙare a kanta. Wannan aure duk dangi suna farin ciki dashi, Jabu zata dawo cikin danginta." Dan a wannan lokacin labarin soyayyarmu ya bazu, Hama kuma kamar mahaukaciya haka ta zama. Dan soyayyar da muke ma juna ni da Yaya Hamma soyayyace wacce baki bazai iya faɗeba, alƙalami bazai iya rubutashi ba. Idaninmu a rufe suke ruf. Duk wani bugun zuchiyata ankai an kawo da soyayyar Hamma yake bugawa. Shima nunamun kulawa yake yi irin kulawar da banyi zatonta a wajen bafulacan daji ba. Ina ba Dada Madara a baki tana sha kamar a mafarki saina hango Uwani tafe da Saleem Yana biye da'ita har zuwa gadon da muke. Gabanane ya yanke ya faɗi muka ƙurama juna idanu ni da Saleem babu um babu um_um. Kallon kewa da tsantsar so Saleem yake yi mun. Ni kuma ina mishi kallon tausayi da dana sanin saninshi, domin son maso wani babban ciwone, na ɗanɗani ɗacinshi akan Debisi. Saye Saleem yake cikin baƙar jallabiya wacce ta sake bayyana sirrin kyanshi, gemu, ƙasumba, yalwataccen gashin ido haɗe dana gira, da sumar kanshi su suka zame mishi wani irin adon da suka bashi wani kyau me sanyi, rawanine yane a kanshi mai fari da baƙi, sai baƙin agogo a ɗaure a tsintsiyar hannunshi, ƙafarshi saye da baƙin takalmi me kyau, ga ƙamshinshi duk ya cika wajen . Ana cikin wannan kallon_kallo Yaya Hamma ya shigo shi da Baffa Musa. Uwani ta gaishe da Dada tayi mata yaya jiki. Saleem sai sallama kawai yayi mata, shi ba hausaba, Dada ba turanci ba "Jabu baƙi kikayine?" Cewar Baffa. Shi ko Yaya Hamma gaisawa su ka yi da Uwani tunda dama ya santa. Saleem ya miƙo mishi hannu suka gaisa. Cikin harshen larabci Uwani take mishi bayanin Dada ce mahaifiyata, Yaya Hamma kuma wanane, sai Baffa Musa wan Dada. Tsugunnawa yayi har ƙasa ya gaishesu da turanci. Baffa Musa yace. "Jabu wannan ai sai nake ganin ba bafulatani bane kamar Balarabe ne ko, amman ba larabci yake yi ba?" Yaya Hamma na ɗago na duba. Shima ni yake kallo sai naga idanunshi sun sauya launi kamar yasan abinda ke wanzuwa, dan kallon tuhuma yake yi mun. Duk saina ruɗe na dibibice ainun na kasa amsa maganar Baffa sai Uwani ce tace. "E Baffa Balarabe ne daga ƙasar Saudiyya yazo wajen Jabu. To munje can gidan shine akai mana kwatancen asibitinnan muka tawo" Siraran hawayene suka zubo a idanuna dana kalli Yaya Hamma yana tsaye akan ƙafa ɗaya, ƙirjinshi sai hawa da sauka yake yi. Da sauri na share hawayen nawa dan kawar da zargi, ina cikin tsaka mai wuyar fita, bana fatan in aikata abinda zai sosa ran Yaya Hamma. Yana da mugun kishi akan abinda yake so, a bayama da bai kai ga furta mun so ba yayi kishin Debisi, balle yanzu da maganar Aurenmu tayi nisan da ba da ban ciwon Dada ba da tuni ina ɗakina. Baffa Musa ma yace ana sallaamar Dada daga asibiti washe gari za'a ɗaura auren in yaso daga baya in Yaya Hamma ya gyara inda zan zauna na tare. "Yazo wajen Jabu?" Baffa ya tambaya yana jimamin lamarin. Hamma ya kalla shima, shi dai baice komai ba sai idanu. "E Baffa akwai kayanmu ne a hannunshi na sare_saren dana faɗa muku nayo. Uwani kayanne suka iso?" Na tambaya da sauri ina kashe mata idanu. Uwani ta riga tasan me nake nufi sai tace. "Kaya Alhamdulillah sun iso suna Kano a gidana" Shi kuwa Saleem ni kawai yake kallo. Yaya Hamma kuma ya sauke kanshi ƙasa yana kallon ƙafarshi, sai wasa da ƙafarshi dake kan wadda ya tsaya akai yake yi. "Dada Allah ya ƙara sauƙi. Jabu bari mu ganki mana zamu jiraki a waje" Uwani na faɗin haka ta dubi Saleem tace. "Yalla Saleem" Saleem ya dubi su Baffa yace. "Assalamu alaikum" Yasa hannu a ajjihu ya zaro kuɗinsu na Saudiyya masu tsoka ya ajjiye a gefen ƙafar Dada. Yabi bayan Uwani suka fita. Illahirin jikina ni kuma rawa yake yi. Yaya Hamma na duba, ni yake kallo a lokacin idanunshi kamar garwashi ƙirjinshi ya tsananta hawa da sauka, ya riga yasan akwai wata a ƙasa, dan ance marar gaskiya ko a ruwa zufa yake yi. "Jabu kije ki samesu mana kar ki barsu suita faman jiranki" Inji Dada da bata san dawar garin ba. Kofin madarar na ajjiye da jan ƙafa wallahi na fita. Soyayya gaskiya ce, a wannan lokacin na ji haushin Uwani ainun nasan da gayya tayi maganar domin ita tafi sona da Saleem fiye da Hamma. Ina fita na hangosu a zaune a wani benci, nan na nufesu na isa da sallama siririya a bakina illahirin jikina a mace mus. Murmushi Saleem ya sakarmun na farin ciki. A zahirin gaskiya nasan Saleem yana sona, na yarda da girman son da yake yi mini. To amman Yaya Hamma yayi tasiri a rayuwata baki ɗaya, salon soyayyarshi ya wuce salon da zan tsaya kwatantawa, jin sonshi nake yi tamkar mahaɗin rayuwata. "Alhamdulillah nagode Allah buwayi gagara misali daya sake ƙaddara saduwarmu dake IYABO. Haƙiƙa wannan ranar tana da daraja a wajena." Cewar Saleem kenan dake magana da turanci hannunshi a sama halamar roƙo, haka kanshi yana kallon sama. Ni kuma nama rasa ta cewa. Gabana sai faɗuwa yake yi, tunanina da hankalina yana wajen nemo kalaman da zan wanke kaina dasu a wajen Yaya Hamma. "Iyabo gani na biyoki da batun aurenmu. Inaso a gama komai insan inane matsayata kafin in koma ƙasata, dan in tafi ma da iyayena sahihiyar magana" Ya sake dabaibayeni da wannan kalami a karo na biyu. Shirun nawa yayi yawa, Uwani ce ta zungureni na dawo cikin hankalina, na dubi Uwani ta gallamun uwar harara, na dawo da kallona ga Saleem shi kuma wani irin kallon soyayyar gani kasheni yake yi mun. Ƙofar ɗakin majinyata na duba, Yaya Hamma na hango a tsaye ya kakkafeni da idanu. Da yaga mun haɗa idanu sai kawai ya gyaɗa kanshi ya nufi hanyar ficewa a asibitin da wani irin mugun sauri. Ai saina miƙe ina shirin binshi da sauri. Uwanice ta finciko hannuna ta dangwarar dani a bencinnan na dawo na zauna daɓas. "Wallahi Iyabo ki shiga taitayinki akan wannan Hamman naki abu sai kace taliyar Hausa ke ko kunya ma ba kya ji. Soyayya sai kace asiri, irin auren wahala da ci bayan da kike son yi kenan, a irin ƙauyen da ke kikeson kiyi zaman aure kenan a bukka zaku gudanar da soyayyar? Baki da hankali Iyabo wallahi. Hamma asiri ƙila yayi miki in ba asiriba banga dalilin da zaisa ki maƙale mishi irin haka ba. Arziki na kiranki ke kinfi son ki zauna a talauce. Ki tuno da irin bautar da kikayi a tafiyar aurenki na baya. Jibeshi ƙazamin banza sai tsawo kamar taliyar murji amman a haka kike so. Ji wani irin hawa da sauka na iskanci da ƙirjinshi yake yi wai shi mai zuchiya. Ke kuma da kin ɗibi ƙafa zaki bishi mu ki barmu a gantale a zaune ko?." Murya ta sassauto. "Iyabo kiyi haƙuri ki amshi Saleem a matsayin miji, wallahi zaki ji daɗi. Kiyi tunani ni ƙawarki ce. Ko Dada da kikeson ki taimaka ta dalilin auren Saleem zaki fi samun damar taimakonta. Nasan kina da ƙudirin zama tare da ƴan uwanki ko dan gyaruwar addininsu kamar yadda muka tattauna. Amman Iyabo ai zaki iya saka su a makaranta ba dole sai kece zaki koyar dasu yadda zasu bauta ma Allah daidai ba. Ya fa kamata ki duba" ( ku zaɓa mun miji masoya wannan labari. Ku kanku nasan kun shiga cikin tsaka mai wuyar fita ko? Ina kuma gani Iyabo. Sannan kar kuyi fishi dani akan faɗawa son Hamma da nayi. Hamma ya wuce duk tunaninku. Saƙonninku sun iso gareni ina godiya da soyayya. Akwai wata baiwar Allah data bani dariya da take cewa inna auri Hamma ba zasu yi mun adda'a ba sai dai suce Allah shi ƙara. Wallahi nayi dariya sosai. Ku dai ku biyo labarin kuji ) Anan ƙarshen littafi na biyu ya tsaya. Zamu je hutun kwana goma kafin mu ɗaura daga inda muka tsaya a labarin wasafa farin girki. Yanzu wasan ma zai soma 🙏🏻🙏🏻 Duk mai son turare yayi magana dan Allah da wuri