[10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 25.. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Arewabooks@nazeefah. Ya duba ga mai son books d’ina. Ko wattpad@Nazeefah381. ★📖 Tun da na gan mu a k’ofar gidan duk wata nutsuwata ta kau, sam bana son ha’duwa da mamy sai nake ga hukuncin da aka mata kamar ya yi tsauri, bai kamata a yanke mata hukunci ba tun kafin a tsaurara bincike, ni kaina ba su min adalci ba da suke hora ni ba tare da an yi binciken ba. Da sauri na dawo hayyacina jin wata Uwar tsawa da Hajiya Inna ta daka min. “Fice mu je munafukar banza kawai.” Na runtse idona zuciyata cike da jin zafin sunaye iri-iri da ake kira na da su tun bayan afkuwar lamarin. Na fita da sauri tamkar an hanka’dani jin Uban zagin da Inna ta sauke min. Na tura gate d’in gidansu Mamyn a hankali. Shiru ba kowa as usual, gidan koda yaushe a cikin shiru yake. Da yake basu da wasu yara kuma gida ne na y’an boko da wuya ka ji an yi wata hayaniya mai k’arfi. Inna a ciki ta yi sallamar na san banda ma ta san hukuncin rashin yin sallamar yayin shiga waje da bata yi ta ba. Mama Mahaifiyar Mami da k’yar ta ‘dago ta kallemu kafin naga ta kawar da kanta, ta ‘dan saki tsaki ka’dan. Ta kuma amsa sallamar itama a ciki. A zafafe Inna ta ce “Ba shakka, ai dole ki kalle mu ki watsar Habiba, tunda kun riga kun cucemu me ya rage kuma banda ku zuba ruwa a k’asa ku sha..” Cikin zafin Rai Mama ta d’aga mata hannu “Please Inna ki ja girman ki, bana son ta kai mu ga samun sa’insa, ban ma san me ya kawoku nan d’in ba, tunda dai alak’ar da ke tsakanin mu ya warware kuma ba ‘da tsakaninsu balle kice dalilin d’anki kika zo…” Inna itama a kufule ta furta “Dole nazo Habiba, dole na zo na tambayi makirar y’ar ki dalilin da yasa ta dinga bawa yarinya kayan maye, ai dama ba A’i bace abar zargi ita Fatiman ita ya kamata a tuhuma mu je hujjar da duk dare sai ta ‘dirka mata madara… wato da wannna ta yi amfani ta b’atawa yarinya suna, to sai ta fito mu ji wani k’aton banza ne….” “Ba zata fito ba, Ba zata fito ku saka mata ciwon zuciya ba, ku barta ma da hawan jinin da kuka saka mata, da’din abin akwai Allah akwai kuma hisabi…” Mama ta fa’da tana sake tsuke fuskarta ni kuwa sai gaisheta nake bata ko kalleni ba. Ina ji Inna ta ce “Wallahi sai ta fito ko na saka y’an sanda su fito da ita ta dole, don wannan maganar ba abar da za’a k’yale ba ce ta tafi a banza dole mu binciki wani k’ato ne a hoton can…” Mami da na gani a tsaye ne gabana ya dinga wani fa’duwa fuskarta a d’aure sosai take kallon Inna tana tauna chewingum. Ta zauna tana furta “Ga ni, sai ki gaya min me ke tafe da ku…” Ni kaina ba Inna ba sai da naji shakkar Mami yarda take jijjiga jiki tana tauna chewingum. “Eeh lallai ba shakka, kalarki Zam ta rashin arziki ta bayyana muraran Fatima, dama ashe lumbu-lumbu kika yi mana, kika b’oye wacece ke don kawai ki zaluncemu.” Wani murmushi Mameey ta saki, ta tauna chewingum d’in ya bada k’ara k’as sannan ta turo shi ta yi k’wai da shi. Idonta ta juya kafin ta furta “Hajiya Inna kenan kuma burina ya cika ras! Sai me ya yi saura kuma? Zaku tsireni ne? Ko Police station d’in kika kai ni, baki da hujjar da zaki saka a kama ni da laifi, balle zuwanki police station kamar tona asirin d’iyar ku ne, don duk duniya sai taji labarin abinda ta aikata gwara ma kada ki fara…” Inna wani irin huci take kafin ta furta “Allah ya isa Fateema, In sha Allah sai kin girbi abinda kika shuka, kin zalunci yarinyar da aka baki saboda tausayin rashin haihuwa ashe ke bak’ar muguwa ce makira annamimiya…” Ina kallo Mami ta cije leb’enta ta sake kallon idon Inna ta ce “Kada ki sake zagina, and please ki tattara komatsanki ki bar nan wajen tunda ba abinda ya ha’da ni da ke..” Ni kam ina tsaye kamar an Dasani wani irin hawaye ne kawai yake bulbula a idona, da gaske kalaman Mami sun matuk’ar furgitani Hajiya ta mik’e jikinta a sanyaye ta kalli Mami ta ce “Abinda kika yi Allah ya miki ninkinsa….” “Ameen” Mameey tace tana tauna chewingum d’inta. Idanunta kuwa sai juya su take. Ma fice ina waiwayon Mami na da ko sau guda bata yarda ta k’ara kallona ba, tun bayan kallon farko da ta min. Tun a mota ta cigaba da bambamin masifa. Duka lefin ta tattara ta ‘dora shi a kaina. “Za mu je gidan, don Ubanki zaki gaya min dalilin da yasa ta dinga baki madara baki fa’da ba.” Shiru na mata ina jin abinda take cewa. Sai dai ni sam bata wannan nake ba mamakin da Mami ta bani yafi saka min tashin hankali fiye da masifar Inna. Muna zuwa gida muka tarar Abba ya dawo. Inna tana kallonsa tana amsa gaisuwar sa a ciki. Ta shiga parlorn sa idanunta kuwa sai zubar da k’walla suke. Ni dai ban bi su ba don tsoron Abba nake ji, ina gaishe shi ma da k’yar ya amsa gaisuwata. “Ina kike Munafuka?” Daga tsakargida na jiyo maganar a sama, ko ba’a fa’da ba na san da ni ake, don sunan nawa ya tashi Daga Ayhsa ya koma irin wa’dannan sunannakin. Jikina a salub’e na shiga parlorn Abban na durk’ushe a gabansu. Tana girgiza k’afa ta ce min. “Don Ubanki, yaushe kika yi lalacewar haka da Ubanki da Uwarki ba su sani ba?” K’asa na yi kawai da idona ina zubar da hawaye ba furta “Wallahi Inna ba ni ba ce…” “ke ina wasa da ke ne d’ago ki kalleni ta yaya ya zama ba ke ba ce, ga ki zahiri a hoto.” Na ‘dago ina kallon hoton ina runtse ido, sam bana son ganin wannan hoton. Shiru na mata don na san idan na cigaba da cewa ba ni bace d’in ma babu mai yarda… “Kaga ni ko? Kaga illar ilimin boko ko Imamu? Tun farko da an aurar da yarinyar nan da duk haka bata faru ba, yanzu kun yi bincike a kai ko kuwa zuba ido kawai kuka yi kuna jiran azo har gida a gaya muku an kama shegen k’aton, ai sai yazo mu ji dalilin da yasa ya lallata ta don Ubansa… Don Ubanki a ina yake kuma a ina za’a same shi?” Inna ta fa’da tana kai min duka. “A jiya aka samu nasarar sanin wanene? Sai dai abin mamaki da ya fahimci abinda ya aikata nemansa ake ruwa a jallu wallahi Inna ashe ya gudu tun wancan satin ba kuma a san k’asar da ya tafi ba…” Inna ta runtse ido tana furta “Ba sai a baza police ba, duk inda yake Ai za’a kama shi.” Abba girgiza kai ya yi. Ya furta “Hakan naso a yi Inna, sai dai shi wanda yaso ya aureta da d’in ne, ya ce kada a yi haka don idan har magana ta je wajen police to kamar fa ta kara’de duniya ne, don haka muka saka Dss kawai suke binckiken sirri da ikon Allah kuma za’a kama shi, zaku ma a tuhume shi idan har da gaske saka shi aka yi ba laifinta bane wallahi sai na ‘daureshi na ga Uban da ya tsaya masa.” Inna ta share k’wallarta tana furta “Tun farko abinda ya kamata kenan, sannan kuma tun kafin zancen ya baza duniya dama Imamu ka nemi wani ka bashi ita, a ‘d’aura auren baki alaikum ba wanda ya ji ya gani, don idan aka bari mutane suka farga wallahi ba mai aurenta, duk da dai duniyar ta lallace ba kamar Zamanin mu na da ba.” Abba ya jijjiga kai “In sha Allah Inna ba zata sake ko wata hu’du a gaba na ba, tunda shi da kansa ya fa’da bai ‘dora mata idda ba.” “Ya dai fi!” Inna ta fa’da tana mik’ewa takalmanta ta zura ta ce “Ni zan wuce.” Abba yana kallonta cike da mamaki ya ce “Tafiya kuma Inna? Ai da kin bari sai da safe.” “Bar ni na tafi Imamu, bak’in cikin ganin Hadiza ba zai bar ni na zauna ba, wallahi ko kallonta bana son yi, mata kamar ba jininmu ba, Uwarki Ai na nan tafe zata zo ta sameki da tare ma zamu zo sai ta tashi da mashashshara, haka kawai ki damk’a tarbiyyar y’arki a hannun kishiya, wa yake haka sai kace wani a zamanin Annabawa, ba gashi yanzu ta cucekiba, ai har abada kishiya sunanta kishiya wallahi koda yaushe burinta ta cusa miki bak’in ciki, koda kuwa zata dinga goyaki kullum don tsabar soyayya to kullum zuciyarta da tsanar ki da haushinki take kwana, shashashar banza.” Umma lumshe idanunta kawai ta yi hawaye na zurara daga kwarmin idonta. Ta mik’e don raka Inna ita da Abba. Wannan ya bani damar tashi da sauri na shige cikin d’akin da a yanzu yake amsa sunan nawa. Mayar da k’ofar na yi na kulle sosai. Sai sannan naji wani kuka na tashin hankali yazo min. Ai kuwa na dinga yinsa ba k’akkautawa kamar zaa zare min rai, ranar dai kam ba abinda zan ce ya shiga bakina, tsabar rashin jin da’din da nake ji a zuciyata haka ya bayyana har saman harshena wani d’aci nake ji, na ji bana sha’awar shan ko ruwa, duk abinda ake min baya damuna kamar yarda Mami ta amsa da bakinta wai ta aikata duk zargin da ake mata, ita ta gurb’ata min tarbiyyata, wannan magana ita take dugunzuma tunani na. Cikin dare jin na kasa barci, hakan yasa na mik’e na isa toilet na tsakargida na d’aura alwala na dawo d’aki. Salloli na dinga yi sosai. A sujjada na dinga kaiwa Allah kuka na da rok’onsa ya bayyana min gaskiya a cikin barcina ko a farke, ya bayyanawa iyayena gaskiya akan cewa bani da laifi. Bayan na idar da sallahr na da’de sosai ina salatin Annabi da karanta Wa Ufawwidu Amree Ilallah… kafin na kwanta ina danna Carbin hannuna…. Cikin barcin na dinga wani irin mafarki sai dai kamar zahiri. Wai gani a wani duhun daji, ba gida gaba ba gida baya kuma baa ganin komai sai duhuwa… ina gudu ana bina sai ihun neman ceto nake daidai zan fa’da wani rami na ji an cafko ni ana dariya. Wani mutum ne sai dai bana iya ganin fuskarsa sai muryarsa da ta kara’de dajin yana furta “Ni ne Mijinki AYSHA har abada ba wani bayan ni….” A razane na farka daga barcin cikin wani irin tashin hankali jikina sai kakkarwa yake ina fitar da wani irin gumi kamar dai abinda na gani a cikin barcin zahiri ne, har a lokacin kuma muryar mutumin ko nace Aljannin tana min amsa kuwwa cikin kunnuwana me kenan? Me wannan mafarkin yake nufi? Me ake son a shaida min? Kada dai fa Aljanni ne ya aureni yake son ya hana ni aure kamar yarda naji ana fa’da idan Aljanni ya aureka? Mu ha’du a comment section…🤣🤗 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA… 23 NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ https://chat.whatsapp.com/EuW3Jn8UkDrJudA1ThiH23 Kina buqatar kayan kitchen Masu kyau da rahusa? Kina buqatar inda zaki dinga samun kaya Masu quality? Uwar gda Amarya Duk ku tawo 💃🏽 Quality shine takenmu 😻 Muna maraba da masu sayan daya ko sari 👯‍♂️ Muna tura kaya ko ina da yardar Allah cikin Aminci😻 muna zauna a garin Kano cikin kwaryar birni👯‍♂️ masu sayan kayanmu Mina godia👯‍♂️ *******★ Abokina… ya sake furtawa muryarsa na shaking. Yatsunsa yake matsawa cikin na juna. Daga haka bai sake iya furta kowace kalma ba, sai ajiyar zuciya da ya sauke. Babansa ne ya fara magana ransa a b’ace ya ce “Ka bu’de baki Ahmad ka yi mana bayani yarda zamu gamsu, abokinka kamar yaya? Shi abokin naka a ina ya san AYSHA har ya baka hotunanta.” Runtse idonsa naga ya yi sai kuma ya bu’de su yana kallona ka’dan cikin b’acin rai ya girgiza kai. “Magana ake maka Ahmad?” Babansa ya sake furtawa wannan karan muryarsa na bayyana b’acin ran da yake ciki. “Ka gaya mana gaskiyar lamari kuma wallahi na samu sab’anin abinda ka fa’da ranka ne zai b’aci sosai.” Shiru kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya d’ago idonsa da maik’on k’walla ka’dan wanda basu kai ga zubowa ba sai dai sun ka’da sun yi jajur. Ya datse gefen lips d’insa da alama baya son bayar da labarin don dai sun tilasta masa. Muryarsa cikin wani irin yanayi ya ce “Komai ya faru lokacin da ya rage bikin mu saura kwanaki biyar cif. Ina kwance a d’akina bayan mun gama waya da AYSHA na samu kiran abokina. Isma’il abokina ne da muka yi makarantun primary da secondary tare. A tare kuma muka je gidan su AYSHA ranar da aka d’aura mana aure. Ya ce “Ahmad akwai matsala fa!” Haka ya ce min. Da sauri na amsa “Isma’il matsalar me kuma?” Sai naga wannan kamar hoton matarka ne ko?” Na waro ido ina kallon hoton da ya turo min cikin tashin hankali ganin da gaske AYSHA ce a ciki rungume jikin wani k’aton mutum. Jikina na rawa na ce “Isma a ina ka samu hoton nan?” Ya yi shiru da alama baya son gaya min ne. Sai da na saka masa tsawa cikin tashin hankali na ce “Ba zaka gaya min ba?” Ya ce “Ahmad ka kwantar da hankalinka, ni kaina da naga hoton na yi mamaki sai da na yi zooming sannan na tabbatar itace kuma wanda ya nuna min hoton ya ce sunanta AYSHA kuma sun da’de a tare suna ma’amala ba kuma hotel d’in da baya kai ta…” Jiri naji yana d’ibana sosai da sosai na ce “Ka tabbata Isma ba wani bane ya biya ka ka yiwa AYSHA yarfe, idan haka ta kasance duk duniya ba mai hanani a yi maka d’aurin rai da rai…” Shiru ya yi sai kuma ya ce “Ka bari a bi komai a hankali ni wallahi ba wanda ya saka ni, a wayarsa ina scrolling pictures na gani. Na ce masa na santa ya rantse min ba mu’amalar da basa yi, ya gaya min shi ya fara saninta y’a mace…” k’it na kashe wayar cikin tafasar zuciya. Na dinga jin kamar zuciyata zata fito. Kashegari da kaina na samu Isma na rok’eshi akan cewa ya saka mutumin duk sanda suke tare ya masa vedio ya turo min don so nake na sake tabbatarwa ba AYSHA ba ce. Haka kuwa aka yi Isma ya kira shi ya kuma nuna masa da k’arya yake, shi kuma Irin mutanen nan masu son k’ure mutum da alamunsa don haka ya ce Idan Isma yana so ya tabbatar ya bar wayarsa a kunne yau da misalin sha biyun dare. Ai kuwa sai ga Vedio still ya turowa Isma shi da AYSHA suna ba’dala har da cup d’in madara yana shayar da ita tana kwance jikin sa… “ D’aga haka Ustaz ya yi shiru hawaye na bulbula daga idonsa… ni kuwa kallonsa kawai nake cikin mamakin abinda yake fa’da. Ban tab’a sanin Ustaz mugu bane sai yanzu ashe duk yaudarata yake ya zo ne don ya b’ata min suna. Kukan ma ya k’i zuwa saboda matsanancin tashin hankali da nake ciki. Ina kallon Jikin Umma kakkarwa kawai take tana nuna Mameey amma bakinta ya kasa furta abinda take son furtawa. Abba kuwa wani irin ajiyar numfashi yake saukewa yana rik’e kansa. Su Yaya Muhammad ba wanda ya iya motsi a cikinsu. Daddyn Ustaz da yaga abin na gida ne sai kawai ya mik’e ya ce da Ustaz su tashi su tafi ya kalli Abba yana fa’din “Alhaji abu komai a hankali, yaran yanzu ne ka haifesu baka haifi halinsu ba. Ubangiji Allah ya shirya mana zuri’a.” Ina kallo ya fita hannunsa rik’e da na Ustaz da naga kamar jiri na ‘dibansa…. Sai sannan Yaya UMAR ya yi wani irin kukan kura ya cafko ni ya fara wanke ni da mari, tun ina gani har naga bana ganin komai sai duhu. Na kuma kasa Kukan saboda tafasar da zuciyata take min. Da sauri Mami tazo zata janye ni. Abba ya daka mata wata irin tsawa da ta sa kowa ya yi tsit a parlorn. Murya a kausashe ya ce “Sakar min y’ata Fateemah! Azzaluma macuciya! Kin cuceni kuma ba zan tab’a yafe miki ba, Allah ya isa!” Cikin duhun idanu na na dinga kallon yarda Mami take runtse ido tana taune leb’enta ta furta “Ya isheka Imamu! Na gaya maka ya isheka! Ya za’a yi ka dinga tuhumata da laifin da ba nawa ba? A gidan Uban wa nace AYSHA ta lallace ko na san tana lalatarta a b’oye? Ta ya zan san abinda take aikatawa a b’oye. Ka saurara min ko don an ga bana haihuwa shine kuke tunanin zan lallata y’ar kishiya?” Ta fa’da muryarta na sark’afewa da wani irin kuka mai k’arfin gaske. Tsaki Abba ya ja ya furta “Idan ma ta tabbata ke ce, to wallahi ki tabbata kin tattara kin bar min gida kafin na san hukuncin da zan yanke a kanki.” “Saki nake so Imamu idan ka tashi sakin nawa ka min saki Uku, haka kawai zaku jingina min laifi…” Umma dai na gefe tana runtse idonta fuskarta ta bayyana tashin hankalin da take ciki. Ya.Muhd ne ya kalli Abba idanunsa na zubar da hawaye ya ce “Abba ka bari mu ji ta bakin wannan munafukar yarinyar? Uban waye wannan d’in? Don da alama sun da’de da shi don ga kayan shaye shaye nan Suna sha, daga ganin wannan madarar abin maye ne a ciki, ji fa idanunsu…” Madara? Ita na ji ta zo kai na, na bu’de kumburarrun idanuwana da bana son sake ganin abinda suke cikin hoton, amma hango cup d’in madarar sai na tuna da madarar da Mami ta dinga d’ibga min kafin tariyar bikina. Ya.Muhd ya kai min wani duka ya furta “Don Ubanki ba magana ake miki ba? Na ce Uban waye wannan d’in? Sannan har shaye shaye kike ko?” Da sauri na girgiza kai na na ce “Ni bana shan komai wallahi, ni ban san komai ba na san dai daf da zuwan bikina Mami tana bani wata madara kullum da daddare da take saka ni barci bayan wannan wallahi ban san komai ba!” Wani irin shiru naji parlorn ya yi. Kowa idonsa a kan Mami da kawai yake kallonsu tana waro ido. Ta kasa furta komai sai kallona take bakinta a bu’de Abba ya wani irin yunk’orowa ya isa inda take. “Fateemah gaya min madarar Uban me kike bawa AYSHA duk dare? Gaya min kafin na datse igiyar aure na da take kan ki…” Ya fa’da yana janta da k’arfin gaske. Ta mik’e tsaye itama a zafafe tana kallon cikin idonsa kafin naga ta saki wani murmushi ta wafce jikinta tana furta “Madarar da zata bugar da ita ta saka ta karuwanci na bata Imamu kuma burina ya cika yau AYSHA ta zama karuwa, ban yi haka don komai ba sai don aurenta da Ustaz ya mutu kuma na samu riba akan hakan……” Ba wanda bai bu’de ido yana kallonta ha’de da jin mamakin furucinta ba, ta bimu da kallo d’aya bayan d’aya kafin ta sake jinjina kai ta fice daga d’akin. Ina ji dai Abba mutuwar zaune ya yi. Umma kuwa idanunta ko blinking basa yi tsabar tashin hankali. Ni dai na san na lumshe ido amma bayan haka ban sake sanin komai ba, sai farka wa na yi na ganni shimfi’de a tsakargida jikina sharkaf da ruwa ba kowa a wajen, sai Yaa Usman da Jummai mai aikinmu suna ta faman yi min sannu. Na mik’e zaune ina jin kaina kamar zai rabe biyu ina kallon Ya. Usman na furta “Don Allah Ya.Usman kace min mafarki nake ba gaskiya ba don Allah.” Hawayen da naga suna sauka daga idonsa ne ya tabbatar min da ba mafarki nake ba. Hannu ya kama ya damk’e cikin nawa ya matsa da k’arfi yana furta “Why AYSHA? Me yasa kika zab’i waccan rayuwar mai matuk’ar muni da ba inda take kai mutum sai tashar nadama? A farko dai mutum yana jin da’dinta kafin ta jirkice ta koma saka mutum Nadama! Why AYSHA duk tarbiyyar da aka baki a gidan nan kin hanb’areta kin dasa wata daban, me kika rasa? Ci sha ko sutura ko kayan more rayuwa? Kowa burinsa a gidan nan samarwa AYSHA farin ciki ashe ke kina nan kina bin abinda zuciyar ki take so. Idan wannan hoton na baya da ya nuna mana a buge kike, AYSHA wancan Kuma vedion a ras ‘dinki kike, amma kike zaune akan cinyar namiji… Ga shi nan Kin ja Abba ya yi mummunan fushi da ke, Umma kuwa ta ce kada na shigo da ke d’akinta gwara ki mutu ta huta… Abba ya saki Mami…” Duk abinda yake fa’da idanuna suna kafe a kansa bana ko k’iftawa. Wani irin zafi da tafasa nake jin zuciyata na yi. Ba abinda ke min yawo a kwanya sai furucin Mami ta ji da’di da na zama Karuwa! Ashe burin Mami kenan a kaina…” Na dinga jin zuciyata na wani irin bugu. Ganin kamar bana hayyacina hakan yasa Ya.Usy bani ruwa na sha, ya kama hannuna muka nufi d’akin Umma, binsa kawai nake kamar rak’umi da akala. Umma na gani na ta wani mik’e da sauri tana kallon Usman. Marairaice mata ya yi sai naga ta yi murmushi ta d’aga masa kai. Hakan yasa ya juya ya fita. Tana ganin ya yi nisa ta ‘dago tana kallona da wasu firgitattun idanunta ta mik’e tana furta “Biyo ni nan munafuka!” K’irjina ya buga na mik’e jikina a sanyaye na bi bayanta. Wani ‘d’aki da muke ajiye shirgi nan ta shigar da ni muna shiga ta mayar da k’ofa ta rufe ruf har da murza mukulli. Ta dubeni a tsawace tana furta “Cire kayanki tas! Bana son ganin komai a jikinki sai Brezier da pant… “ na bu’de ido ina kallonta muryata na rawa na ce “Don Allah Um…” “Rufe min baki munafuka! Wani abu zaki b’oye a jikin naki? Wanda duniya bata gani ba, zigidir kike kwance jikin namiji bakomai a jikinki sai pant…” Ta fa’da a tsawace. Ganin ba alamar wasa tattare da ita yasa na cire kayan nawa. Wata irin waya na gani ya ciro a bayanta ta shiga lafta min a jiki. Tun ina ihu har na saduda na yi shiru, don muryarta ma ta daina fita… Tana gama ta cillar da bulalar duk da magi y’ar da su Jummai suke mata bata bu’de ba, ta juya tana kallona “Kuma ki bu’de kunne da kyau ki ji ni, daga yau duk aikin gidan nan ya dawo kan ki… idan wancan hoton a buge kike d’ayan vedion fa ras da k’afafunki muryarki garau kina furtawa wani banzan namiji zantukan ba’dala, Kun cucemu kin karaya zuciyar mahaifinki munafuka!” Daga haka ta fice na runtse idona kukan ma ya k’i zuwa sai tafasar zuciya. Ina jin Jummai ta d’aura min zani na har hawaye take tana furta “Ya Ilahi wani irin duka ne wannan? Bari Usman yazo ya kai ki asibiti.” Tana fita kiran Ya. Usman na mik’e ina layi na zura rigata “Ba Zan iya ba guduwa kawai zan yi na ayyana haka a raina. Duk jikina ra’da’din zafin dukan yake…… [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 24. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Ina saka kai tsakargida Ya.Usman shima yana shigowa hankalinsa tashe yake kallo na. Kafin na ga ya kama hannuna da sauri ya ja ni muka koma cikin d’akin. “Ina zaki Aysha?” Shine tambayar da ya fara jeho min. Madadin na amsa masa wani hawaye ne ya shiga suntiri a kumatuna. Ya zaunar da ni yana kunna fitilar d’akin. Wani guntun tsaki ya ja, yana furta “Nan Umman ta kawo ki? Anan d’akin shirgin zaki kwana?” “Usi ba wannan tambayar ya kamata ka mata ba, ka kamata mu tafi asibiti ji fa jikinta yarda duk ya yi Shatun Bulala. Sai sannan ya kalli jikin nawa da sauri naga ya waro ido yana furta “Ya Ilahi! Tashi AYSHA tashi mu tafi asibiti.” Na mik’e da k’yar ganin ina layi yasa Ya.Usi ya kama ni muka fita zuwa tsakargidan. Turus ya yi Jin Umma ta ce “Gidan Uban wa zaku? Usman ba zaka fita shirgin gallafirin yarinyar nan ba?” Fuskarsa a tsuke ya ce “Umma abin ya yi yawa, ji fa jikinta ji yarda kika mata rauni da bulala.” A zafafe ta ce “Sai me? Sai me don na raunatata ba gwara na illata jikin da take tak’ama da shi wajen jan hankalin mazan ba, ba wani asibiti da zaku wuce ki koma ciki. Kai kuma idan ka sake ka bita ban yafe maka ba..” Ina ji cikin sanyin jiki Ya.Usman ya zame hannunsa daga cikin nawa, ya wuce zuwa part d’in su. Wasu zafafan k’walla ne suka shiga zubo min, Ina ji Umma ta sake jan tsaki ta koma d’akinta. Jummai ce ta ja hannuna idonta fal k’walla muka koma cikin d’akin da muka fito. D’akin ta tsaya tana kallo na san ba mamakin da take sai ta yarda Ni AYSHA y’ar gayu zan kwana a d’akin nan, da aka tabbatar da ba komai a cikinsa sai shirgin b’eraye da muk’arebansu. “Ko zamu je zan wajen mu ki kwana AYSHA kafin komai ya lafa.” Jummai ta fa’da na girgiza mata kai na, na ce “Bar ni kawai Jummai, bar ni na kwana a inda Umma take son na kwana, fata na Allah ya ‘d’au raina a daren nan na huta….” Da sauri Jummai ta saka hannu ta rufe min bakina. “Ki yi shiru AYSHA kowane bawa baya wuce k’addararsa, kawai ki yi ta istigafari Allah gafururruhimu ne, duk girman laifin ki matuk’ar kika yi tsarkakakken tuba zai yafe miki…” Ido na k’ura mata cikin jin mamakin lafazin bakinta, kenan itama Jummai ta yarda ni zan aikata zina. Madadin na bata amsa takaicin da yake cin zuciyata ya hana ni kawai sai na lumshe idona ina zurarar da hawaye. Jummai ta mik’e ta fita daga d’akin sai gata ta dawo da bargo da zanin gado har da pillow ta mik’o min. Karb’a na yi na saka a gefena ta min sai da safe ta fita bayan ta bani panadol. Ban bi ta kan maganin ba, don ba buri na waraka ba ni ban k’i na mutu a ranar ba. Har jiri nake ji tsabar jigata da rashin cin wadatacen abinci tun bayan afkuwar lamarin. Alwala na samu kai na da fita yi kamar an tuna min a wannan gab’ar Ubangiji ne kawai gatan ki Aysha. Na shiga toilet d’in masu aiki duk da k’yama ta a ranar neman k’yamar na yi na rasa na fito na d’aura alwala a famfon tsakargidan mu. Na koma d’akin da a yanzu ya zama mallaki na. Sallah na tayar na dinga jerata ina kaiwa Allah kuka na a cikin sujjada da son ya agajeni ya tona asirin duk mai hannu a cikin wannan sharrin da aka min. Don dai na san ba ni ba ce, ba zan kuma tab’a yarda da ni d’in ba ce. Ban kwanta ba sai k’arfe uku da kwata na dare. Kiran sallahr farko kuwa Umma ta banko k’ofa ta tashe ni. Da k’yar na bu’de idona ina kallon yarda take min kallon tsana ta furta. “Fito y’ar banza lokacin hutu Ai ya k’ure miki, fito maza ki ha’da wutar kunun sadaka ki kuma wanke wake na k’osan sadaka. Don na gayawa su Jummai wannan aikin daga yau ya dawo kan ki, wanke wanke da shara kawai za su dinga yi.” Wani irin kallo nake ma Umma kallo mai cike da mamaki kamar ina tantamar zamowar Umman Mahaifiyar da ta tsuguna ta haifeni. Bata bi ta kan kallon da nake mata ba ta mik’e ta fice. Jikina ciwo yake matuk’a da gaske amma hakan bai hana ni tashi na isa inda ta ce na je d’in ba. Ba tun yau ake koko da k’osan sadaka ba a gidanmu. Don haka na san duk inda su Jummai suke yi musamman kasancewata mace mai son girki. Tukunya na ‘dora a wuta babbar gaske mai cin kwano goma. Sannan na dinga d’ebo ruwa a bokiti in zubawa sai da na zuba bokiti uku na paint. Na ha’da wutar da k’yar su Jummai dai suna tsaye suna kallo na da Umma ta ja kunnensu akan bata amince su taya ni ba. Sannan na koma kan wake kwano biyar na ‘debo don ma a surfe yake shi yasa ban sha wahala wajen wanke shi ba. Ina gama wankin waken aka yi kiran sallah. Na zame jiki da k’yar na je na tada sallahr ina hawaye saboda matsanancin ciwo da jikina yake yi. Ban bar gaban murhu ba sai k’arfe goma na safe zuwa lokacin duk wanda ya ganni sai ya tausaya min, lokaci guda duk na fita daga hayyacina kamar ba Ayshan Mami ba. Sha d’aya na kwanta, bayan na idar da sallahr walaha. Barci awa guda na yi Umma ta shigo wannan karan hauri na tayi da k’afa na bu’de idona da k’yar ina kallonta. “Uban wa zai d’aura abincin ranar?” K’asa na yi da kaina kawai, ina jin wani irin k’una da zuciyata ke yi. Sai naga ta fita kawai tana furta na baki 30 minutes ki fito ki d’aura abincin. Tsabar yarda zuciyata ke suya ma bai saka na yi hawayen ba, idona kawai na lumshe ina jin wani irin tsanar Ustaz na zagaye jiki da zuciyata, duk shine Sila da bai shigo rayuwata ba da duk haka bata faru ba, tabbas ha’duwata da shi ba abinda ya jawo min sai tashin hankali ya wargaza farin cikina ya wargaza na ahalin gidan mu. Wannan masifa har ina? Me yasa idan na ma aikata Ustaz ba zai min uziri ba sai kawai yazo gidanmu ya tona min asiri? Na dinga ha’diyar zuciya ina jin kamar zuciyar tawa zata daina aiki. Haka na mik’e ganin mintuna talatin da Umma ta bani sun cika, sauk’in abin ma girkin ranar na iya gida ne kawai kuma akan gas ake yin sa. Amma ina fitowa sai Umma ta kalleni ta ce Sakwara za ki yi. Da sauri na ce “Sakwara kuma?” Ta zuba min harara ta ce “Eeh pounded Yam, ita Abbanku yake so kuma dakan turmi ba engine ba…” Jingina na yi kawai da bango ina bin bayanta da kallo ina sake tambayar kai na Anya kuwa Umma ita ta kawo ni duniya?” Tun daga ranar ban huta ba, Umma jibga min aiyuka take masu yawa da suka fi k’arfina. Tun ina jin ciwon jiki idan na yi har na saba ganin bata da ranar dai nawa kamar ma k’ara ingiza ta ake. Na yi bak’i na rame na yi wani irin lalacewa, idanuna suka shige lungu kamar ba AYSHA y’ar gayun Mami ba. Sam Umma bata barina na yi wanka sai bayan kwana biyu abinda yafi damuna kenan daga izayar da take min, don ni kam ina da son wanka a lokutan baya kafin abin ya faru na kan yi wanka Three times a day wallahi. Yanzu kuwa babu damar haka na zama kamar wata y’ar fursuna tsanar yarda jiki na ya lallace don ma fatata mai kyau ce. Rabona da na saka Abba kuwa har na manta, balle su Yaya Muhammad. Ya.Usi ne sam baya fushi da ni, ya kan zagayo duk. Dare ya mik’o min d’an abu a leda ko nama ko yoghurt sai dai baya min magana, hakan kuma da yake ban damu ba don na san yana bin umarnin Umma ne. Da safiyar wata juma’a, lokacin sati biyu cif da faruwar lamarin, Ina zaune a tsakargida Jummai ce take gyara min kai, sai jin sallamar mutane na yi, ko ba’a fa’da ba na san wacece zuciyata ta buga da k’arfin gaske don na san wacece Muryar Kakata ce da ta haifi Abba, wacce muke kira Inna. K’asa na yi da kaina ina jin yarda zuciyata ke harbawa. Jummai ce ta amsa sallamar, ta amsa a ciki sai sannan na ‘dago na ce “Inna sannu da zuwa…” wani irin kallo ta watso min da yasa hantar cikina ta ka’da na santa sarai mace ce mai zafin gaske, don ko wasan jika da kaka ita ba yi take ba, kullum girarta a tsare ta ke da k’yar ta kan yi murmushi shima ba ya zarce gefen lab’b’anta. Ta yi k’wafa ta shige parlorn Abba ba tare da ta amsa gaisuwata ba. Umma jikinta na rawa naga ta fito daga d’aki. Ta shiga parlorn Abban itama. K’walla min kiran da ta yi ne yasa hantar cikina juyawa jikina kamar mazari na mik’e na shiga parlorn Abban. A gefe ba durk’ushe tun kafin ma ta ce min na durk’usa ‘din. Masifa ta cigaba da yi. “Dududu A’in nawa take da za’ace kun kasa bata tarbiyya, Mace guda d’aya jal da Allah ya baku a ce baku san hanyar da zaku tarbiyyantar da ita ba! To dama da nazo bai saki annamimiyar can ba da Allah ka’dai ya san abinda zan muku, haba ni tun a farkon fari ban so ya auri matar nan ba, kana ganinta kaga wayayyiyar da idonta ya Riga ya bu’de da duniya ga shi nan ta gurb’ata muku tarbiyyar y’a da son ranta, ai kuka jawo da kika d’au y’a guda mace da Allah ya baki kika bata, kika kuma ja gefe kika daina saka baki a tarbiyyarta wai ke alkunya, yanzu wa gari ya waya? Wa aka cuta idan ba ke ba? Ga Boko nan Ai kun gani da an yi magana Imamu ya ce wai Fateemah y’ar boko..” Ta yi k’wafa tana cije leb’enta ta ce “Wallahi bata ci bulus ba, yanzu zan je har gidan Uban da ya d’aure mata wani wuri na ci Ubanta la’ada waje har na ha’da da iyayenta iskancin banza da wofi…” Cikin rauni Umma ta ‘dago tana kallonta ta ce “Inna ba za’a yi haka ba, tunda dai ya saketa Ai bai kamata ki je ba…” “sai na je Kubra… ina ce Fateemah ba k’anwar Uwarki ba ce balle ta Ubanki kuma bamu da alak’ar komai da ita tunda bata haihu ba ko? To sai naje, sai ta gaya min dalilin da ta yasa ta saka yarinya a turbar rashin arziki… Ke kuma annamimiya tashi mu je maza ki nuna min gidan, kafin mu dawo ki gaya min abokin shai’danancin naki shima na je har gidan Ubansa na ci mutuncinsu….” Zufa ce ta dinga zubo min, ni kuwa me yasa Inna zata ja ni gidan su Mami ni sam ba zan iya kallo Mami ba, duk da abinda ta min har yau da tausayinta a raina, sai dai sam ban isa na yiwa wannan jarababbar matar musu ba. Jikina a salub’e na mik’e ba bi bayan Innan da take ta min masifa… “Allah dai ya wadaran boko, ba ga abinda nake gayawa Imamu ba kullum nazo sai nace ya aurar dake ya ce min wani Zamani ya canja, ai gashi nan yanzu yaga zamanin a gidansa…” Ni dai shiru na yi mata. Ko a cikin motar masifar da take ta yi kenan. Idona lumshe har muka isa gidansu Mami. Ina ganin mu a k’ofar gidan gaba na ya yi wani masifaffen fa’duwa…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ https://chat.whatsapp.com/EuW3Jn8UkDrJudA1ThiH23 Kina buqatar kayan kitchen Masu kyau da rahusa? Kina buqatar inda zaki dinga samun kaya Masu quality? Uwar gda Amarya Duk ku tawo 💃🏽 Quality shine takenmu 😻 Muna maraba da masu sayan daya ko sari 👯‍♂️ Muna tura kaya ko ina da yardar Allah cikin Aminci😻 muna zauna a garin Kano cikin kwaryar birni👯‍♂️ masu sayan kayanmu Mina godia👯‍♂️[10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 26… NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION. ★★✍️ Bayan na koma barcin still wani Mafarkin na sake yi ana sake k’yakyata min dariya ba k’akkautawa. Ina gudun ana bina na durk’ushe a wajen ina wani irin kuka ba na komai ba sai na neman taimako, ina kuma addu’ar Allah ya raba ni da koma menene mai bi na d’in… A kusa da ni aka yi maganar da ta kusa saka ni na zauce. “Ba ki da mafita Aysha, baki da mafitar da ta zarce addu’a, idan kowa ya k’i ki mu muna son ki…. daidai nan na mafarka sakamakon dukan da Umma ta kai min a gefen cikina. A firgice nake kallon Umman da itama ta k’ura min ido, kafin naga ta d’an janye idonta da kaina, idan ba idona ba ne ya gano min ba daidai ba, sai naga kamar k’walla ta share. “Ki tashi an yi sallah ki fita ki yi aikin ki…” ta fa’da cikin raunin muryar da ta sake sanyayar min da jiki. Na mik’e jikina a salub’e na fita na yi alwala. Ko da gari ya waye na gama duk Ayyuka na, sai na ji zuciyata ta yi sanyi bayan idar da sallahr walahar da ta zame min jiki. Na zauna ina sake tariyo mafarki na, na ji a raina tabbas na amince da cewa Aljannu ne suka aure ni, suka fito min ta wannan hanyar. Ina son na je na gayawa Umma amma zuciyata na kwab’ata don haka na k’udundune maganar na barta cikin raina, dafatan Allah yasa naga Ya.Usi na gaya masa mafarkin ko ya samar min mafita. Da yamma kuwa ina kitchen Yaya Usman ya shigo. Ina ganinsa na saki murmushi alamar farin cikin zuciyata ya kasa b’uya. Ledar hannunsa ya mik’a min kafin ya furta “Ta samu kenan ko Aysha naga fuskarki fal fara’a.” Murmushin na sake yi ina furta “Ya.Usi dama tun safe nake nemanka.” Ya k’araso wajena yana murmushin don yanzu da sauk’i Umma ta daina hana shi yi min magana. Ya furta “Gaya min Aysha me ya faru?” Na gyara tsayuwata ina ajiye wuk’ar da nake yanka cabbage. Na ce “Ya.Usi na gano wanene ya min duk sharrin da kuke cewa na aikata…” Da sauri ya ce “Wanene Aysha gaya min na je naci Ubansa!” Na d’an girgiza kai kafin na ce “Aljanni ne Ya.Usi, Aljanni ne…” Kallon da yake min ne yasa ni ha’diye sauran maganar, gaba d’aya idanunsa sun bayyana rashin yarda da zance na. Amma sai naga ya saki murmushi ya girgiza kai ya ce “Aljanni kuma Aysha? Ta yaya kika san Aljanni ne duk ya aikata hakan?” Idona na ji suna tara k’walla kafin na fara bashi labarin mafarkin da na yi. Shiru ya yi yana kallo na kafin ya saki ajiyar zuciya ya ce “Mafarkin Aysha zai iya zama Aljanni zai kuma iya zama ba Aljannu ba, zai iya zama wani abu Allah yake so ya nuna miki, amma duk da haka ba zan bar maganar haka ba, zan samu Umma da maganar idan yaso sai na kai ki wajen ruk’iya don a yi miki a duba idan da Aljannin ko babu..” Na d’aga kai ina furta “Na gode Ya.Usi” muryata a shak’e. Ya mik’e min ledar hannunsa abinda ya saba kawo min ne time to time yau d’in ma ya kawo min. Yoghurt ne mai sanyin gaske da kazar yahuza. Cikin farin ciki na sake masa godiya ina kallo ya juya zai tafi. Yana furta “Idan kina son mu cigaba da shiri, ina son ki zama Good girl, ki yi ta istigfari kin ji…” Gaba d’aya jikina naji ya yi sanyi ganin da gaske shima Ya.Usi bai yarda da ni ba, yana kula ni saboda shi mutum ne mai sanyin hali ba kamar sauran y’an uwana ba. Na tuna ranar da ya rutsani da son na gaya masa gaskiya. Rantsuwa na masa da girman Alk’ur’ani akan ni dai a hayyacina ba wani namiji da ya tab’a rik’e min ko hannu bayan Ustaz.” Shiru ya yi sai kuma yasa hannu yana shafe min tarin k’wallar da take zubo min. Ashe dai Yaya Usi duk abinda na fa’da har yanzu bai amince da ni ba. Yanzun ma kukan na yi na kuma share hawaye na ba tare da kowa ya lallashe ni ba. Bayan sallahr Isha’i, sai ga shi ya shigo d’akina. Jikinsa a sanyaye ya furta “Zo Aysha mu je ki k’ara maimaita mafarkin ki a gaban Umma, ina fatan wannan ya zama k’arshen wahalar ki.” Na mik’e ina addu’a a raina, Allah ya biye bakinsa ya sa k’arshen wahalata ne ya zo. Ko da muka isa ya fara gaya mata, kafin ya ce Aysha gaya mata irin mafarkin da kika ce kin yi..” Na gyara zama na shiga gaya wa Mami ina gaya mata murya ta tsaf ba don komai ba sai don ta yarda da ni. Wani kallo ta dinga min, kallon da ya dinga saka ni jin kamar jijoyin jikina suna tsinkewa tsabar sanyin da gab’ban jikina suka yi. Wani murmushi ta yi ta ce “Aljanni ko? Kai kuma Usmani sai ka yarda da labarin k’anzon kuregenta, mak’aryaciyar banza, ka zauna ta wahalar da kai a banza…” Yaya Usman fuskarsa ta nuna rashin jin da’din abinda Umman ta ce ya ce “A’a Umma, kada ki ce haka ki bari a je a ji ta bakin Malamin kafin ki yanke hukunci duka zancen AYSHA zai iya zama gaskiya fa….” Umma ta tab’e baki ta ce “Ai ban hanaka ba Usmanu, abu guda na sani k’arya take kuma zaka ce na gaya maka, b’ata lokacin ka kawai zaka yi… amma ma ji ma gani wai an bawa mai kaza kai.” Daga haka ta shige d’akinta ta bar mu ni da Ya.Usi fuskokin mu cike da damuwa, da gaske lamarin Umma mamaki yake ba ni. Yaya Usman ya ja hannuna a fusace, Yana furta “Mu je Aysha, Allah ya bayyanar da gaskiya a lokacin kowa zai gane abinda aka miki baa kyauta ba.” Wani murmushi na saki ina raya ranar kuwa da kallo don babu wanda zan ragawa, don ni ba a tausaya min ba a lokacin da nake son a tausaya min. Za su sha wuya k’warai da gaske kafin su shawo kai na.” A machine d’insa muka tafi gidan Malamin da zai min ruk’iya. Babban Malami ne k’warai da gaske,wanda ya shahara a b’angaren cire Aljannu. Muka ci sa’a kuwa babu kowa sai mutum biyu kacal a wajen. Daga ganin Malamin zaka san addini ya ratsa shi. Bayan Yaya Usman ya gama gaya masa abinda ya kawo mu, sai ya umarce ni nima akan na sake masa bayanin irin mafarkin da na yi. Ban yi nawar baki ba na sanar da shi komai. Da duk abinda na gani a cikin barcin. Cikin ta’ajjabi yake girgiza kai yana kallo na ya ce “Usmanu tabbas zai iya zama Aljannu ne da k’anwarka, zai iya kuma zama bata da Aljannin wani lamari Allah yake son bayyana mata a cikin barcin. Ba zamu gane hakan ba sai ta hanyar Ruk’ya, kana ganin a yi mata yanzu babu matsala?” Usman ya girgiza kai ya ce “Ba matsala Ya sheikh, sai dai da zai yiwu na fi son a yi a gida a gaban iyayenmu don su tabbatar duk abinda aka ce ‘din da gaske ne…” Malam ya girgiza kai ya ce “Haka ne, yanzu abinda za’a yi zuwa da safe In sha Allah ka min kwatancen gidan naku zan je na yi mata In sha Allah a can, tabbas wannan lamari akwai sark’ak’iya a cikinsa.” Ya.Usi ya yi godiya ni ma godiyar na masa, sannan muka mik’e muka tafi. Da muka je gida wani irin kallo Umma ta mana sai kuma naga ta yi murmushi ta ce “Usmanu, har an cire Aljannun? Guda nawa aka cire?” Usman ya d’an tsuke fuskarsa murya a cunkushe ya ce “Baa mata ba sai gobe zai zo a yi a nan, amma fa Umma bana jin da’din yarda kike yiwa AYSHA sai kace ba ke kika haifeta ba, kin banzagatar da lamarinta, komai ta yi Ai kamata ya yi ki ja ta a jiki ki ji dukkan matsalolinta.” K’asa naga Umma ta yi da kanta sai naga hawaye na ‘diga a idonta ta girgiza kanta ta shige d’aki ba tare da ta yi magana ba. Ya Usman ya kalleni ya girgiza min kai kawai shima ya ce “Aysha Umma na son ki, kuma tafi kowa son dukkan abinda ya faru ya zama sharri, a hakan da kike ganinta dauriya kawai take tana cijewa abinda yake damun zuciyarta yana da yawa Aysha. A idanun Umma nake hango tausayinki da k’aunarki..” Na share hawayena Usman ya ce “Ki tashi ki tafi ki kwanta ki huta.” Ban musa masa ba, don tabbas ina buk’atar hutun na zuciya k’wak’walwa da gangar jiki gaba d’aya. Don haka na shige d’akin da ya zama mallakina. Kashegari k’arfe tara na safe Ya.Usman ya shigo da Malam Sitroom. A tsakargida Abba ya fito daga sashensa yana furta “Ka kiyaye ni Usman, wani Aljannu ne da Aysha da zaka kawo min Malami gida?” Ya.Usman ya marairaice hakan yasa dole Abba ya shige sitroom d’in. Nima Ya.Usman ya ce na mik’e na shiga. Da sallama na shiga parlorn cikin zumbulelen hijabi na mai tsaho da fa’din gaske, irin wa’danda na saba ta’ammali da su… Malam yana kallo na ya ce Sannu Ayshatu Baiwar Allah, In sha Allah yau Ubangiji zai nuna mana gaskiyar lamari…” Sosai na ji da’din kalaman Malam, Saboda cikin tausayawa da tausasawa ya yi furucin. Na ayyana dama haka iyayena suke min da zuciyata bata shiga cikin k’unci da ciwon da take ciki yanzu ba. Malam yasa na mik’e k’afata kafin ya ce Ya.Usman ya rik’e manyan yatsuna na k’afa guda biyu. Ya dubi Abba ya ce. “Alhaji kada ka yi mamaki a ce maka duk wani abubuwan shai’danun Aljannu ne suka aikata, suna yin fiye da hakan, Ubangiji ya yassare musu wannan baiwar ta riki’da dukkan suffar da suke..” Abba ya girgiza kai yana furta “Allah yasa hakan ya kasance.” Malam ya ce hakan ne ma In sha Allahu.” Sannan ya fara rero karatun Ruk’iyyar….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 27. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Tsawon rabin awa Malam yana karatun, sai dai ko gezau ba abinda na ji, ba kuma abinda ya canja a jikina. Malam ya dubeni ya ce “Ayshatu ba ki ji wani sauyi a jikin ki ba? Ba ki ji tsigar jikin ki ta tashi ba? Ko jiri da ciwon kai haka?” Na girgiza kai na da sauri na ce “Ban ji ba Malam.” Sai na ga ya bu’de wata kwalba ya yarfa min wani turare a cikinta.. wani irin turare mai warin gaske mai hauka kai. Tsawon mintuna biyar yana kallon cikin k’wayar idona. Sai na ga ya girgiza kai yana sakin ajiyar zuciya ya kalli Abba ya ce. “Abin mamaki, Alhaji ba Aljannu a jikin yarinyar nan.” Abba ya saki wani malalacin murmushi wanda daga ganinsa ka san na b’acin rai ne da karayar zuciya ya furta. “Dama Allah ya gafarta Mallam, don kada ka ce na k’i yarda da abinda kazo da shi ne, amma ni na san ba wani Aljanni a jikin yarinyar nan, shai’dananci ne kawai irin na yaran Zamani. Da kuma tsagwaron ta rainawa mutane hankali ta zauna ta shirya zancen wai ta yi mafarki.” Ya ciji leb’ensa yana bi na da kallo. “Ga shi nan yanzu kun yarda da kan ku, na yi mamakin kai da Usmanu da kuka yarda da tatsuniyar yarinyar nan wanda dama k’arshenta shine k’urunk’us! Ta shi ki ba mu waje Munafukar banza…” Tuni murna ta ta koma ciki, wani sanyi ya ziyarci zuciya da gabban jikina, na dinga jin rauni a tare da ni. Ban san ya aka yi na kai kaina bakin k’ofa ba, ina ji dai Malam yana cewa “Alhaji ku bita a hankali, tsangwama da kyara ba shi zai gyara ta ba sai addu’a da kuma janta a jiki.” Lumshe idona na yi ina datse leb’ena ba don komai ba sai don zantukan Malam sun tabbatar min da cewa, shi ma ya yarda ni d’in tantiriyar y’ar iska ce. Hakan ya sa wani hawaye ya dinga sulmiyo min na ayyana yanzu haka shi ma Yaya Usman daga rana irin ta yau ya fita daga sabgata shikkenan na tabbata Ni Ayshatu Na ga rayuwa. Umma ko ko bi ta kaina ba ta yi ba bayan wani banzan kallo da ta yi min da na fito daga parlorn Abban ta furta “An cire Sarkin Aljannun a kan ki? Haba wa ni na san ba ta yarda za’a yi Aljanni ya rab’i zuriyata ba alfahari nake ba, amma addu’oin tsarin da nake muku tun kuna ciki da girmanku ba zai bar Aljanni ya kusanceku ba, sai dai idan ke ce Aljannar kan ki.” Tun daga ranar ban sake saka Yaya Usman a idona ba. Ba ya nemana ledar da yake kawo min ma tuni ya daina kawowa. Wannan shine abinda ya fi d’aga min hankali. Ranar yau Asabar Anty Khadija matar Ya.Muhd da matar Ya.Sadik suka zo. Da murna ta na tare su cikin tsananin farin ciki. Anty Khadija ma da fara’ar ta rungume ni tana kallon jibgegen zanin gadon da nake wankewa da brush a tsakargida. Sai naga ta d’an jijjiga kai kawai fuskarta a tsuke ta ce “Asysha ke kike wanke wannan kuma?” Ban bata amsa ba na yi murmushi kawai na juya ina kallon matar Ya.Sadik da take bina da wani kallon banza tana yamutsa baki. “Ina yini?” Na furta cike da mamakin kallon da take min. Kamar wacce aka yi wa dole ta amsa tana d’age kai. Ba tun yau na fuskanci sam Yaya Sadik bai dacen mata ba, tana da isgili girman kai da izza. D’auke kaina na yi ina kallo ta shige cikin part d’in Umma na saki ajiyar zuciya kawai. Ji na yi AntyKhadija ta kama kafa’data ta furta “AYSHA idanunki kenan ko? Ko kunya babu ki ke kallona?” Na d’an saki baki, don ban san dalilin kalamin nata ba. Ta yi dariya ganin kamar na d’an firgita ta ce “Eh mana, yanzu yaushe k’afafunki su taka gida na? Tun ranar da Ustaz ya je ya d’auke Matarsa…” wani irin runtse ido na yi jin abinda ta ce. Sai naga ita ma ta dafa kanta ta furta “Oh Am Sorry Sisi, ni kai na bana son ambaton sunan mutumin can wallahi na tsane shi shi kuma Yayanku ya kafe ba laifinsa ba ne, ko shine a shoe d’insa abinda zai aikata kenan, yanzu dai ba wannan ba, yaushe za ki kawo min ziyara?” Ajiyar zuciya na saki, don kam ta famo min wani miki a zuciyata. Ranar d’aurin aure na da Ustaz ya je gidan Ya. Muhammad da duk abinda ya faru. Na lumshe idona kafin na bu’de su na ce “Zan zo duk ranar da Umma ta yarda.” Tana dariya ta ce “Ai kuwa yau zan tambayi Umma ta barki ki je, ko kya huta don na ga duk kin rame kamar ba Ayshatu y’ar Gaye ba.” Ta kira ni da sunan da Brothers d’ina suke kira na. Na d’an yi murmushi kawai jin abinda ta ce. A zuciyata kuwa addu’a nake Allah yasa Umma ta bar ni na je gidan Anty Khadija don macece mai karamci kuma ina sonta sosai. “Idan mun dawo d’aga kai lefe kawai sai mu yi tafiyar mu, In sha Allah zuk’eken mijinki na hanya wanda zai so ki da dukkan aibunki…” cikin mamaki nake kallonta na ce “Lefen wa za’a kai yau d’in?” Wani kallo take min ta ce “Baki san za’a kai lefen Umar da Usman ba yau?” Wasu k’walla na ji sun zubo min kawai na girgiza mata kai ina sunkuyar da kai na. Jikinta a sanyaye ta dafa ni, sai naga ta kasa magana ta cije leb’enta kawai ta shige parlorn Umman. Na runtse idona ina jin sautin zuciyata yana tashi daga normal zuwa wani irin bugu da ya dinga ba ni tsoro. Ba komai nake tsoro ba sai bana son ciwon zuciya ya kama ni. Tunani nake shi ma Ya.Usi ya daina ta tawa kenan shi yasa har aurensa zai zo bai gaya min ba. Tsabar ciwo da kaina yake da rawa da jikina yake da k’yar na samu na gama wankin na mik’e na shige d’akin da nake ina fasa wani irin kuka mai saka k’unci da ciwo a zuciya. Kafin yamma kuwa gidan mu ya cika taf da mutane. Ina daga cikin d’aki ina jiyo hayaniyarsu sai dai ko da wasa ban yi gangancin shiga cikinsu ba. Na yi zama na a d’aki. Idona a lumshe don ko waya bani da ita tunda abin ya faru Abba ya saka Ya.Muhd ya k’wace wayar. Ji na yi an turo k’ofar d’akin da nake. Anty Khadija ce a tsaye tana kallona tana bin d’akin da kallo kuma duk a lokaci guda. Ta ce “Ke ba zaki fito ba ne AYSHA? Ki shirya a tafi ganin lefen da ke, wai ma me ki ke yi a store?” Wani malalacin murmushi na saki kafin na ce “Ba store ba ne, yanzu nan ne d’aki na Anty Khady.” Sai naga ta waro ido ta furta “Ah haba wasa ki ke, sai kace wacce ta yi kisan kai?” Ta d’an shigo tana sake k’arewa d’akin kallo. Ina kallon yarda take dakiya tana k’ok’arin kada k’wallar da take idonta ta zubo. “Tashi mu je, dole yau idan mutane suka watse zan yi wa Umma maganar ta bar ki koma gida na. Dama Arfa ta fara isata da saka magana ga shi kwanannan laulayi ya saka ni a gaba.” (Arfa yarinyar su ce da suka haifa na manta ban gaya muku ba.) girgiza kaina na yi na ce “Ku je kawai Anty ba inda za ni bana son shiga mutane.” Tana shirin sake magana aka turo k’ofar d’akin. Zinatu da Zaituna suna tafe suna wata irin shewa. Ina ganin su na mik’e zumbur daga tabarmar da nake kwance. Idanun su cikin nawa ba su yi magana ba har sai da suka gaishe da Anty Khady ta fice daga d’akin tukunna sannan suka juyo waje na. Zannira y’ar Umma Dije k’anwar Abba da yake bin sa. Ita kuma Zinatu y’ar k’anwar Umma ce Umma Sa’a. Da yake na gaya muku Abba da Umma first cousins ne auren zumunci aka musu. Sarai na san Zinatu da Zaituna basu da mutunci k’warai da gaske kuma a kansu Abba yake fa’da da iyayensu don kamar yarda ba su da kunya suma iyayensu ba kunyar ce da su ba. Inna ta sha fa’da min an sha fama da iyayensu suna y’an mata har sai da aka aurar da su ba shiri, sai ga shi sun haifo kwafinsu tsaf ko a ce wanda suka fi su. Ba sa wani zuwa gidan mu amma lokacin bikina suka zo suka tare a gidan sun doshi kwana goma da su aka yi komai a bikin. Duk da ban wani saba da su ba, Abba ya k’i bari na na saba da su don baya sake musu fuska. Da murmushi na tare su, sai dai ga mamaki na sai naga sun wani zuba min harara suna min kallon banza. Zannira ta turo baki tana furta “Oh! Ikon Allah sai kuma ga karuwa a gidan Ashsheikh Imamu, waliyyin Allah!” Da sauri na waro ido ina kallon su, jin wulak’ancin da suka shirya yi min. Suka tuntsire da dariya Zinatu ta ce “Gane min hanya Zannira, yanzu kuma ban san ya zai yi ba? Mutum duk ya bi ya takura mana akan d’an shan Mintin da muke da samari, sai ga shi y’arsa tana abinda ya ci Uwar na mu, zigidir a kan cinyar saurayi da kayan maye, kai wannan abu ya yi min sugar na so na ga Idon Shehi Imamu ranar….” Wani irin kukan kura na yi na maku’reta da k’arfin gaske ina haki ina huci idona duk sun ka’da sun yi jajur, tun Zinnira na ganin kamar zata iya k’waceta ba tare da kowa ya ji ba har taga abin ya gagareta da sauri ta fita tana ihun a kawo d’auki jama’a AYSHA zata kashe Zinatu. Duk wasu jama’j da suke gidan suka yi yo dandazo zuwa d’aki na. Sai dai na k’i sakin Zinatu, ranar kam kamar an k’ara min k’arfi. A mak’ure nake da ita ina mata wani irin kallo. Anty Khadija na ji ta ja ni jikinta hakan yasa na kwanta lamo a jikin nata ina sakin wani irin kuka cikin kukan na bata labarin abinda ya faru… na kuma lumshe idona na ce “Anty a yanzu bayan Mami su ne mutane na biyu da nake zargi akan wancan vedion, ai ba k’arya na ne kowa yana fa’da ina kama da Zannira sosai da sosai jikin mu farcen mu duka iri guda ne, fuskar ce dai nake tunanin tawa suka saka a gangar jikin Zanniran!” Tsit na ji mutanen d’akin sun yi idanu kuma suka koma kan Zannira da cikin wani irin razani take ware ido tana pointing d’ina da yatsunta…. JIKAR NASHE★✍️ [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 30.. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ Ki tashi mu tafi na ce miki Aysha!” Ya.Usman ya fa’da cikin muryar da ke bayyana fushinsa. Girgiza kaina nayi na ce “Ya Usman ka bar shi ba zasu fahimceka ba suma a potiskum d’in, ka bar shi na yarda da k’addara zan Jure, zan auri Tanimu.” “Ba zaki jure ba AYSHA, hauka ake za ki auri Tanimu, ki tashi mu tafi na ce.” Hawaye ne suka zubo min na ce “Ya.Usman, Umma fa? Baka ganin ranta zai b’aci kuma zata yi fa’da.” Fuskarsa a tsuke sosai ya finciki hannuna da kansa ya zura min Hijabin ya ja hannuna muka fice da sauri. Motar gidan mu da Driver yake ja ita Yaya Usman ya tura ni a ciki. Ya tayar da ita da sauri muka bar gidan cikin wani irin mugun speed. Ni dai lumshe idona kawai na yi saboda sam raina babu da’di. Har muka isa garin kuma magana jefi-jefi muke yi, duk da tafiya ce muka yi ta bata wasa ba. A cikin gidan kuwa Inna da fara’a ta tare mu, ta saka aka kawo mana abinci da ruwan sha da zob’o masu sanyi. Kasancewar daga ni har Yaya Usman ba mu karya ba hakan yasa muka ci abincin sosai. Da alamu Inna ta fahimci rashin nutsuwa a tattare da mu, don haka bata mana magana ba har sai da muka ci abincin muka yi sallah kuma. Sannan ta ja ajiyar zuciya tana kallon Yaya Usman ta ce “D’an fodiyo tafiyar lafiya kuwa kuka yi na gan ku ficikai ficikai. Ba nutsuwa sam a tare da ku.” Yaya Usman, ya kalleta ransa a b’ace ya furta “Ba lafiya ba Inna, haka kawai k’alau kin san ba zan yi yo wannan doguwar tafiyar ba.” Ta girgiza kai ta ce “k’warai kuwa, da dai Muhammadu ne shine bawan Allah mai son zumunci, sai ka gaya min me yake tafe da kai?” Ya sake tsuke fuska ya ce “Yanzu Inna abinda ake wa AYSHA ya dace akan laifin da ba a tabbatar ta aikata ba, kada fa nan gaba a zo ana jin kunyar yarinyar nan..” Inna ta ‘dago kai tana kallonsa “Duk na yi wannan tunanin bayan dawowata Usmanu, kuma ina shirin na koma a wannan satin na ce a je can gidan su Fatiman. Rok’eta Allah da annabi a ji da gaske yarinyar nan ta san tana aikata ba’dala kamar yarda Kakanku ya ce min, sai kuma ga ku kun zo yanzu me ya faru kuma?” Usman ya ce “Wai aure Abba zai mata, auren ma na son k’ask’anta ta wai da Tanimu Driver…” Inna ta ce “Cabd’i jam! To lamarin Imamu kuma sai du’ai, ta ina wannan abin yazo masa fisabilillah kamar muna garin mahaukata, to ba da ni zaa yi haka ba tozarcin Ai ya yi yawa. Zata yi aure dai amma ba da Tanimu ba da kai na zan samar mata Mijin aure dama can abin yana raina, na ce ko da yaron nan, Alhaji da kansa ma ya yi sha’awar hakan da Miftahu za’a ha’data aure Jikan Mariya k’anwata yana da halinsa kuma zai iya rik’eta In sha Allah, na san zai rufa mana asiri..” Yaya Usman ya saki ajiyar zuciya yana furta “Wannan kuwa, In dai Muftahu ne ai sam ba shi da aibu, Allah ya tabbatar mana da alheri, amma don baki ga gallaza war da ake mata a gidna can ba kamar wacce ta yi kisan kai.” Inna ta tsuke fuska ta ce “Kayya, amma Kubra akwai ragowar Imani kuwa a tattare da ita? Sai ka ce ba ita ta haifi y’ar ba, ai shikkenan sai ta yi zamanta anan har lokacin aurenta ta yi aurenta su tafi can lagos da Miftahun.” Yaya Usman ya kalleni sai na sakar masa murmushi don har a zuciyata na amince da auren Miftahun, don ba laifi kyakykyawa ne Fulani Usuli kuma d’an gayu ne ya yi bokonsa daidai gwargwado. Shigowar Alhaji kakanmu ce tasa aka yi shiru a d’akin. Da mamaki yake kallo na ya ce “Tsohuwa ke ce yau a gidan?” Murmushi na saki ina gaishe shi ya yi dariya ya furta “Shikkenan amaryata ta zo bari a bu’de miki naki d’akin ki shiga..” Jan mu ya dinga yi da wasa har na mance kaso hamsin na b’acin raina sai b’abbaka dariya nake. Tsaf Inna ta gaya masa duk abinda yake tafe da mu. Sai naga ya yi dariya ya ce “Imamu kenan, wato masifaffiyar zuciyarsa tun ta yarinta har yanzu yana nan yana fama da ita, ban da abinsa wa yake tsallake k’addararsa idan ma ta aikata d’in ta dawo ta tuba Ai sai a yafe mata, Allah Ai gafururrahimu ne. Dama ko baku zo ba ni na yi niyyar kiran Imamun na gaya masa a k’arshen watan nan za’a d’aura mata aure da Miftahu jikan Mariya, tunda kuwa kun zo sai ka barta anan su fahimci juna da Miftahun kai koma.” Usman ya mik’e yana duban agogo ya ce “Ai yanzu ma zan juya, don baa san mun taho ba.” Suka yi sallama nima na raka shi har mota ina jin kamar na yi hawaye don tafiyar da zai yi. Ya girgiza min kai murya a hankali ya ce Be a good girl AYSHA, In sha Allah k’arshen matsalarki ne.” Na lumshe idona ina cije leb’ena ka’dan na d’aga masa kai ya saka hannu ya share min hawaye na sannan ya dank’a min ku’di masu d’an yawa a hannuna ya shiga mota yana d’aga min hannu. Jikina a salub’e na koma gidan. Sai dai yarda Alhaji ya tasa ni a gaba da hira da abubuwan ban dariya yasa na wartsake na shiga amsa masa. Ina wajen Alhaji ya kira Abba ya fara yi masa fa’din kan hukuncin da yaso yankewa ba tare da neman shawara ba. Abba dai shiru ya yi sai da Alhajin ya gama fa’da sannan ya ce “ka yi hak’uri Alhaji, hankalina ne duk a tashe game da lamarin yarinyar nan ta kai har bana son shiga taro…” “To sai me shi d’an Adam Ai dama haka yake, ba ya raina abin fa’da don haka maganar wani Drivern ka na janyeta, na soketa daga yau yaron nan Miftahu zata aura…” wata ajiyar zuciya na ji Abba ya sauke wadda kana jin sautin fitarta har ta cikin wayar. Ya ce “Alhamdulillah, Allah yasa Midtahun ya amince..” Alhaji ya ce “MIFTAHU yaro ne mai biyayya na san ba zai ja da umarni na ba.” Suka yi sallama. Sai sannan na mik’e na fita tsakargida don taya Inna aiki. Da daddare a kan gadon Kakata na kwanta, cikin matuk’ar kwanciyar hankali da samun sukunin zuciya. Murna ta cika ni ganin na fita daga k’angin bauta zuwa y’anci da nake fatan ya ‘dore har gaban abada. Kamar an ce na kai Sunnah T.V na danna remote na kai, abin mamaki kawai sai ga fuskar Ustaz ta cika allon television d’in, fuskarsa da ‘dan murmushi ka’dan yana kallon wanda yake karanto masa tambayoyi yana amsawa kamar yarda ya saba a duk sanda ya gabatar da karatun da yake gabatarwa duk juma’a da lahadi. Cak lumfashi na yaso d’aukewa sai dai na yi jarumta k’warai da gaske wajen ganin ban rasa nutsuwata ba. Hannu na saka zan kashe t.vn sai na ji mai tambayar ya ce “Ustaz Ahmad ita wannan tambayarta guda ce, wai me yasa ka saki matarka a daren da ta tare a gidanka?” Shiru Ustaz d’in ya yi yana murza goshinsa da d’an yatsan hannunsa kafin ya furta “K’addara.” Ya kuma lumshe idon bai sake magana ba. Da sauri na danna remote na kashe Tvn zuciyata na wani irin tunzira da wani irin b’acin rai. Na lumshe nawa idon ina jin kwararar hawaye a saman fuskata. Har cikin dare na kasa barci saboda k’unar da zuciyata take ciki ba zai bari na samu na yi barcin ba. Shi yasa da na Yi sallahr asuba Inna ta ce koma ki kwanta ki dai ina jin ki ba wani barcin kirki kika yi ba, wato ba zaki bar sakawa kanki damuwa ba ko?” Shiru na yi don bani da amsar da zan bata. Dole na koma barci don idona har yaji yake. Da safe na diga jiyo hayanyia daga parlorn Inna sama sama. Da sauri na mik’e don sai na ji kamar fa’da ake. Na d’an d’aga labulai d’akin sai na ga Gwaggo Mariya ce k’anwar Inna take ta masifa idonta a rufe. “Wallahi ba zai yiyu ba Yaya, ta yaya sai da yarinya ta gama watsewarta za’a ce Miftahu ya aureta me yasa sanda take da mutuncin ba a bashi aurenta ba sai yanzu to gaskiya da sake ba dai Miftahu ba… ina shi ina auren Karuwa fisabilillah Miftahun da kowa ya shaida da nagartar halayensa…” D’if parlorn ya yi ana saurarar tijarar gwaggo Mariya da ko kunyar furta wasu maganganun bata ji. Ni dai ji na yi kai na yana wani irin sarawa ga duhu ina gani ga wata irin hajijiya ni dai daga nan ban sake sanin me ya faru ba sai gani na yi a kwance a gadon asibiti. Inna a zaune kusa da ni sai Alhaji shi kuma yana zaune kan kujera duka fuskokinsu ba sukuni don Inna ma kamar kuka take.. ido na na sake lumshewa don bana son su fahimci na farka ina ji Alhaji ya ce “Yanzu ba zaki shiru da kukan nan ba…” cikin shashshek’a ta fara magana “Bar ni Alhaji, bari na yi kukan nan ko zan samu zuciyata ta yi sanyi, Mariya fa! Mariya tawa ita take gudun ha’da jini da ni saboda wata k’addara ta samu jinina ashe Mariya ba mai iya rufa min asiri ba ce? Jikanta take cewa ba zai auri Jikata ba wani irin Zamani muke ciki?” “Irin wanda Manzon Allah ya bamu labarin zai zo, don haka ki saka a ranki ba lallai yarda zuciyar ki take ba ta kowa ta zama haka fak’at! A yi addu’ar Allah ya kawo mata Miji na gari kawai.” Zuciyata ce take wani matsanancin bugu wai ni yau Ayshah ni ake talla da ni ana k’in aure na? Wace irin k’addara ce wannan tabbas jarrabawar nan zata min wuyar answer don ina jin karaya tun daga zuciyata har gab’ban jikina…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 29. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. ★★✍️ Umma ta juya ta fita ta bar d’akin ba tare da ta sake min second look ba. Jikina a sanyaye na mik’e na bi bayanta ina fatan duk da abinda za su zo min yazo min da sauk’i. Sanda na yi sallama duka a ciki suka amsa min sallamar. Fuskarsu a mutyuke musamman Baffa Mutari sai ka rantse da Allah bai tab’a dariya ba. Ina zama Baffa Mutarin dai shi ya fara magana muryarsa a kaurare ya ce “Ke duba nan, duk nan kin san ba abokin wasanki ba kuma sa’anki ko? To ki bu’de kunne ki ji da kyau abinda za mu gaya miki, bana son wasa da hankali kuma, a ina zamu samu abokin shai’danancin ki? Abu na gaba mun yanke hukuncin aurar da ke da zarar kin gama iddar da ta zama dole a kanki, duk da shi ya ce bai d’ora miki idda ba sai dai mutane ba su san wannan ba… ba zaki mayar da mu mutanen banza ba, kina ji ko?” Jikina a sanyaye na ‘d’aga kai. Ya girgiza kai yana yin k’wafa ya ce a haka kamar wata mutuniyar kirki, ki gaya mana a ina zamu samu wancan mutumin banzan?” Hawaye ne ya fara son zubo min na yi k’arfin halin hana shi zubowa. Wata tsawa da ya saka min ban san sanda na runtse ido ba na furta “Zan fa’da wallahi.” Baffa Yahya ya yi wata dariya ya ce “Kin ceci kan ki don wallahi da ba ki fa’da ba yau idan na dinga dukanki a gidan nan sai kin kasa tashi.” Wani irin huci suke fitarwa hakan ya sake tsorata ni a hankali na ce “Wallahi Allah ban san shi ba…•” wani irin mari Baffa Yahya ya kai min suka cigaba da zagina. Ni dai ina durk’ushe ina zubar da wasu irin hawaye ina kallo suka gama ci min mutunci suka fice. Na mik’e tun kafin Abba ya bani dama na shige d’akina cikin rawar jiki da bugawar zuciya. Haka rayuwa ta cigaba da gargara min, wasu abubuwan tuni na saba da su yayin da wasu abubuwan har a kullum sake firgita ni suke yi. Ta gefe guda na samu sassauci a wajen Umma da Abba suna amsa gaisuwata duk da dai ba sakin fuska a tare da su. Yayyena ma su kan d’an kula ni ka’dan. Hakan ya saka na d’an samu sauk’in zuciya. Sai dai ba dama na fita an dinga zun’dena kenan a cikin unguwa hakan yasa na rage fita. Dama ba Bari na fitar ake ba Umma dai ta daina gallaza min da kaso talatin cikin d’ari. Hakan yasa na d’an samu nutsuwa ta wani b’angaren. Wani dare Abba ya dawo tun daga yanayin yarda yake tafiya na san ba lafiya ba. Kamar jiri yake ka’dan fuskarsa ba walwala ko ka’dan. Na masa sannu da zuwa ya ‘dan amsa min yana d’auke kai na karb’i ledar hannunsa shi kuma ya shige cikin sasansa. Ina zaune a tsakargida Umma ta fito tana kallo na ta furta ki je In ji Abban ku.” Da sauri na mik’e duk da zuciyata ta yi wani irin bugawa na isa wajen Abban. Yana zaune idanunsa akan t.v ya zuba ido yana kallon labarai. A gefe na durk’usa nima ina kallon t.v ‘din ba tare da ya kalleni ba ya ce “Ki je waje zaki gana da bak’on da na zab’a miki a matsayin Miji, kada kuma ki sake ki bujircewa Umarnina a yayin da idanunki suka yi tozali da abinda bai gamsheki ba…” Zuciyata ce kawai take bugu na mik’e jikina a sanyaye ina tunanin waye Abba ya zab’a min a matsayin Miji, sai dai ina tunanin koma waye zan jure zan kuma yi biyayya na amsheshi da hannu biyu ba don komai ba sai don na faranta ran Abba. Ban koma d’aki ba da dogon Hijabi na na fita harabar gidan. Ba kowa a harabar daga Idi mai gadi sai Tanimu driver. Isa wajensu na yi ina furta “Sannunku, don Allah ina wanda ya zo wajena.” Sai na ga Tanimu ya mik’e yana washe baki, ya furta “Ai ba wani ba ne Hajjaju ni ne…” Cak na tsaya ina kallonsa sanye yake da koriyar shadda da hula orange sai yage hak’ura yake kamar me, babu aji sam a tare da shi, ni da nake son mutum d’an gayu miskili mai ilimi mai iya soyayya da kalamai masu kwantar hankali ta ina zan iya da Tanimu? Na dinga cijar leb’ena ba tare da na san ina yi ba. Ya kuwa cigaba da gyara tsayuwarsa yana furta “Anan zamu tsaya ne Hajiya Aisha, akwai maganganun da nake son na rattabo miki….” Samun kaina na yi da tafiya da baya da baya ina girgiza kai na. Hawaye kuwa suka fara zuba kamar famfo… ina ji Tanimu na kira na sai dai nan tsaya na saurareshi ba na shige cikin Gida da sauri. Karaf na ji na yi karo da mutum… da sauri na ja baya ina mayar da numfashin da naji yana min wuyar fita kamar ana shak’e min mak’ogwaro. Da sauri na ji Yaya Usman ya rik’e hannuna yana furta “Nutsu Aysha menene me ye ya baki tsoro haka?” Hannuna na saka na dinga nuna masa waje sai dai baki na ya kasa furta abinda nake son fa’da masa. Gani na yi kawai ya ja hannuna mun nufi cikin gida. Sai da muka isa d’akina ya zaunar da ni, sannan ya tsiyayi ruwa a cup ya saka min a baki. Ruwan na sha sosai kafin na saki ajiyar zuciya ina kallonsa na lumshe idona hawaye yana zubo min daga ido na ce “Yaya Usman wai Tanimu Driver Abba ya bawa aure na. Wallahi Yaya Usman wannan karan ba zan jure ba, da na auri Tanimu gwara na bar gidan nan na bi duniya ka….” Da sauri ya saka hannu ya rufe min baki, yana furta “A’uzubillah!!! Kina da hankali kuwa AYSHA kin san abinda kike fa’da kuwa? Ba kya cikin hayyacinki ko? Ki nutsu ki min magana yarda zan gane, waye ya ce miki za ki auri Tanimun?” Cikin shashshek’ar kuka na ce masa Abba ne Abba ne da kansa ya ce ya bashi aure na…” Yaya Usman ya zaro ido ya ce “Ah haba wallahi wannan karan hakan ba zai yiwu ba, ko kisan kai kika yi Ai sai haka? Akan wani dalili ina matching a aurenki da wani Tanimu? Ina zuwa zauna anan yanzu zan dawo…” ya fita da sauri duk ransa a b’ace binsa na yi da sauri na rab’e a jikin windown parlorn Abban ina jin abinda Yaya Usman d’in yake fa’da. Ina ji Abban ya amsa sallamar yana furta “Usmanu yaya dai?” Yaya Usman ya gyara zama ya ce “Abba wata magana na ji AYSHA ta gaya min, wai ka bawa Tanimu aurenta, Haba Abba Ai abin zai yiwa AYSHA yawa, sam babu matching a ha’din, Abba ka yi tunani da kyau, Tanimu mara ilimi AYSHA mai ilimi Tanimu d’an k’auye Ayshatu y’ar birni, Tanimu marar wayewa AYSHA mai wayewa, ta ina wannan ha’din gambizar zai hadu fisabilillah, Haba Abba ku tausaya mata don Allah dama itace namijin shi mace sai a ce ha’din zai tafi don Allah Abba ka yi hak’uri kamar hukuncin ya yi tsauri da yawa…” wani murmushi na ga Abba ya saki ya ce “Ka gama Usmanu? Na ce ka gama? Duk na ji abinda ka ce abu guda da ka manta baka fa’da ba a banbancin na su shine Ayshatu y’ar iska Tanimu kamilalle, ashe ba Tanimun aka cuta ba da za’a lik’a masa ragowar wani? Idan ba mu godewa Tanimu ba bai kamata mu tozarta shi ba, don haka maganar aure babu fashi fak’at bana son na sake jin wata magana bayan ta ta amince da zab’i na, idan ba haka ba d’aga kai Har AYSHA wallahi za ku har gidan nan…” wata irin harbawa zuciyata ta yi da sauri na bar wajen cikin matsanancin tashi hankali. A daren ranar dai ban sake ganin Yaya Usman ba, yarda na ga dare haka na ga rana zuciyata ba abinda bata sak’a min ba na aikata sai dai na kasa yarda na gudu na bar gida. K’arfe shidda na safe Yaya Usman ya shigo d’akina yana kallona ya ce AYSHA tashi…Tashi tashi mu tafi potiskum don Abba ya rantse a gobe zai d’aura miki aure da Tanimu da zarar manema auren sa sun zo… ki tashi ba mu da lokaci….” Wani irin kallo nake masa ido na ko blinking basa yi tsabar ka’dawa da zuciyata ta ke. Ji nake kamar wasu abubuwan basa aiki a Gangar jiki na… AURE DA TANIMU? Shine abinda zuciyata take ta nanata min… 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 28. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. A razanen ta cigaba da nuna ni muryarta na rawa ta furta “Sharrin da za ki min kenan Aysha, wallahi k’arya take Sam ba ni ba ce a jikin hoton nan kuma ba ni da alak’a da duk wani abu da ya shafi hoton…” Bori na hau yi Anty Khadija na rirrik’eni na hau nuna su ina fa’din wallahi su ne, na gaji na gaji don me za’a dinga jingina min laifin da ba nawa ba ne,Hakn ya isa! Ya isa!! Ya isheni!!! Runguma sosai Anty Khadija ta kai min ta saka hannunta ta toshe min baki. Ki yi shiru Aysha Allah yana bayan mai gaskiya kuma tabbas shi zai saka miki. K’ananan maganganu ne suka cigaba da tashi a d’akin kowa yana fa’dar duk kalmar da yaga dama a kaina. Umma dai na tsaye tana bin kowa da ido. Zannira ta turo baki. “Ah to yarinya kada ki sake kama suna na, abin kunya ne dai kin janyowa familyn mu, kuma kina nema ki lik’a mana, nan kika dinga kwanaine kina hura hanci wai ke za ki auri mai ku’di ke da ake gani kamilar mace ake murnar ta samu Miji d’aya tamkar da dubu sai ga shi kin ba’dawa iyayenki k’asa a ido an tashi ba wan ba k’anin abinda Bature ke kira 2-0…” Kowa na ‘d’akin cike da mamaki ake kallon su Zannira jin irin kalaman da suke fita daga bakin su. Umma dai tana tsaye idanunta sun ka’da sun yi wani irin jaa. Anty Khadija ce ta kalli Zannira da Zaituna a zafafe ta ce “Ah to lallai ta bakin AYSHA akwai lauje cikin na’di a cikin wannan habaicin da kuke zubar wa, ashe dai tabbas hassada da bak’in ciki kuke mata, idan kuwa ya tabbata hakan ne ba abinda ba zaku iya aikatawa ba wajen son ruguza maganar auren, don haka dole an bincike ku ku fa’di gaskiya don ba k’ira ba abinda zai kawo gawayi….” A zafafe Umma Sa’a ta ci burki a gaban Anty Khadija ta nuna ta da yatsa.. “Kada ki fara Khadija, kada ki sake ki jawo mana waruwar kai a cikin dangi, mu kan mu a ha’de yake abinda bahaushe ke kira tsintsiya mad’aurinki d’aya don haka ki cire hasashenki akan su Zinatu me ye ribarsu idan suka yi silar waruwar auren AYSHA?” Bu’de baki Anty Khadija ta yi zata yi magana Umma da ke tsaye ta furta “Khadija ya isa! Kada ki sake magana, idan ma abinda kika fa’da d’in gaskiya ne Allah zai bayyana cikin girma da d’aukakarsa…” Shiru Anty Khadija tayi tana mayar da numfashi hawaye na zuba daga idonta, sai dai bata sake maganar ba duk da irin maganganun da suka cigaba da tashi na mita da habaici. Ta yi shiru kawai her face looking so worried. Jan ajiyar zuciya kawai take tana buga baya na. Tsit da d’akin ya yi ne ya sata mik’ewa tana kallo na, ta furta “Ki yi hak’uri AYSHA Allah yana bayan mai gaskiya, zan yi shiru da wannan maganar amma anan kawai ba don komai ba sai don bana son yin jayayya da umarnin Umma, amma zan gayawa Yayanki zaku ma mu cigaba da bincike ta k’ark’ashin k’asa amma tabbas zato na akan yaran nan yake..” Na girgiza mata kai. Ta fice daga d’akin bayan na tabbatar ba zani wajen kai lefen ba. K’una zuciyata kawai take da wani d’aci da nake ji a mak’ogaro na. Ina ji duk aka fice kai lefe. Ya zama gidan ya yi wani irin shiru. Ina kwance idona a lumshe na ji maganar Umma a kaina. “Ke ki zo in ji Abban Sadik.” Ido na na bu’de ka’dan ina kallonta cikin dishi-dishin hawaye na. Itama kallon nawa take sai naga ta juya ta fita daga d’akin. Da k’yar na mik’e saboda matsanancin ciwo da kaina yake. Na yafa mayafi na fita kiran da Abba yake min. A zaune yake fuskarsa sam ba walwala, ba mamaki Umma ta gaya masa duk abinda ya faru. Gefe ya nuna min bayan ya amsa gaisuwata murya a hankali ya kalleni ya ce…. “Me yasa kike zargin su Zinatu da duk abinda ya faru?” A hankali na yi k’asa da ido na ina wasa da hannu na..”Magana nake miki.” Ya fa’da wannan karan muryarsa a sama ka’dan.. shashshek’ar kuka na fara yi ina furta “Nima ban sani ba Abba, kawai ina tunanin zasu iya aikata min hakan daga yanayin kalamansu a kai na.” Ido ya k’ura min kafin ya ce “Wasu maganganu suka gaya miki?” Tsaf na kwashe na gaya masa, sai naga ya yi shiru, idanunsa sun yi wani irin jaa fiye da na Umma. Murza hannunsa kawai yake kafin ya ce “Akwai inda kika je da su ne a satin bikin ki?” Da sauri na d’aga kai na. na ce Eeh Abba akwai, na je gidansu har ma na yi barci a can, mun je kuma gidan Anty Falmata da wasu gidajen na cikin dangi.” Shirun ya sake yi tsawon mintuna biyar kafin ya furta “Tashi ki tafi ki ba ni wuri, Allah ya bayyana gaskiya.” Tunda abin ya faru yau ne kawai Abba ya min magana cikin kwanciyar murya. Sai na ji wani abu ka’dan ya gushe daga b’acin ran da yake cunkushe a zuciyata. Tara na dare na jiyo Yaya Usman ya shigo gidan da sauri na mik’e na nufi har sashensu don tun yamma nake jiransa am eager na ga ha’du da shi. A parlorn dukkansu suke zaune, Ya Usi Ya Umar da Ya Ali. Na gaishesu suka amsa fuskar ba yabo ba fallasa. Ya Usi kam da fara’a sosai ya tare ni. Ya ja hannuna ya zaunar da ni gefensa yana furta “Ya aka yi AYSHA gayu? Koda yake yanzu wannan sunan tsaf ya tashi daga kan ki, duk kin bi kin sukurkuce kamar ba Ayshan Mameey ba…” murmushi kawai na yi ina tuna Mamee a raina. Na ce “Dama murna na zo maka Yaya Usi, duk da dai baka sani a cikin lamarin ba, congrats to you and am happy for you….” Na fa’da wata y’ar k’walla na son zubo min. Kama hannuna ya yi yana furta “Okay Okay na gane, mu je d’aki mu yi maganar har ma na nuna miki hotonta.” Ina mik’ewa muka ha’da ido da Ya.Umar sai na ji bakina kawai ya furta “Congratulations Ya Umar..” Hannu kawai ya ‘d’aga min ina ji Ya.Ali ya zabga tsaki. Muna shiga na zauna gefen kujera ina kallon hoton da yake mik’o min. Yarinya ce k’arama ba zata zarce sa’ata ba. “Ma sha Allah, gaskiya ta yi ina tayaka murna once again, duk da dai baka saka da ni ba.” Hannuna ya matsa yana furta “Am sorry Aysha kwana biyu kin ga bana damuwa nazo inda kike, wallahi zuciyata bata iya wa tausayi kike ba ni, ina so ki tsaya ki nutsu ki ajiye zuciyarki waje guda ki yi aure, da zarar na yi aure zan mayar da ke can waje na, don naga duk gidan nan ba mai tausaya miki na yi magana da Abba akan ya barki ma ki cigaba da karatu ya nuna min sam ba zai yiyu ba, Miji ma yake nemar miki ya miki aure tun kafin mutane su farga da abinda kika aikata, although dai maganar duniya bata b’uya..Wallahi AYSHA da tunanin matsalarki nake kwana nake tashi, ga shi shi kuma shegen an ce har yanzu bai dawo garin ba, bari mu tuntub’eshi mu ji ko biyansa aka yi don ya b’ata miki suna.” Murmushi na saki, irin murmushin da na da’de ban yi irinsa ba, jin abinda Ya.Usi ya ce da gaske shi ka’dai ne mutumin da zan bugi k’irji na ce ya yarda ban aikata ba. Ya saka hannu ya share min hawayen da suke zuba a idona duk da ni ban san zubar su ba saboda har ga Allah murmushi nake. Murmushin na sake yi ina kallon cikin idonsa na ce “Ya.Usi na gode sosai da kulawarka gare ni ya sunan amaryar tamu?” “Sadiya” ya furta yana lumshe ido. “And I love her very deeply….” Murmushi na saki ina ajiyar zuciya a hankali na tuna Ustaz da dukkan kalamansa ashe akwai abinda zai saka Ustaz ya rabu da ni, ko wai wayata bai sake yi ba tun bayan afkuwar lamarin nan, ashe duka soyayyar Ustaz a baki take.” Na girgiza kaina kawai kafin na mik’e na bar cikin d’akin saboda kukan da ya taho min…. Da safiyar wata laraba ina zaune a d’akina sai ga sallamar Asma k’awata. Da wata irin murna na tareta. Ita kuwa hawaye naga ya fara zuba daga idonta. Ta saka hannu ta ja hannuna muka fita harabar gidanmu. “Zo mu je AYSHA, zo mu je kada Umma ta fito ta gan ni ita ta hana ni zuwa duk sanda nazo sai ta ce na tafi kawai..” Na bita muka fita harabar gidan mu. Hawayen kawai take ta kasa ce min komai. Sai da na girgiza ta na ce “Wai Asma’u meye haka zuwa kika yi ki sake d’aga min hankali?” Girgiza kai ta yi tana rungume ni a jikinta ta ce “AYSHA Ustaz ya ci amanar soyayya wallahi, abinda ya miki bai kyauta miki ba, ni fa ban san me ya faru ba sai jiya Umma na take gaya min wai an fara zagaya unguwa da cewa da wani k’ato Ustaz ya kama ki ranar auren ki.” Waro ido na yi zuciyata na bugu na ce “Waye ya fa’da Asma?” Ta sake runtse idonta hawaye na zuba a idonta ta ce “Ba wanda bai ji ba AYSHA zancen nan har Islamiyya wallahi….” Tunda abin ya faru sai yau hankalina ya sake masifar tashi jin ashe zancen ya isa har Islamiyya wajen Malaman da suke ganin mutunci na. “Ki gaya min Aysha ya aka yi kika canja daga Ayshan da na sani?” Runtse idona kawai na yi ba tare da na mata magana ba, don bana jin zan iya furta ko kalmar ‘a’ saboda rawa da dukkan jikina yake yi…” na mik’e dai na shige cikin gida a cikin wani irin yanayi da ni kai na ba zan iya cewa ga yarda na kai kaina d’aki ba. A yammacin ranar still ina kwance, Umma ta lek’o ta ce “Ke ki zo in ji Abbanki da y’an uwansa…” wani irin tsawa na ji kaina ya yi don ban san da me suka zo ba… Kai NI AYSHA NA GA RAYUWA INA KAN GANI MA…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔫𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: https://chat.whatsapp.com/EuW3Jn8UkDrJudA1ThiH23 Kina buqatar kayan kitchen Masu kyau da rahusa? Kina buqatar inda zaki dinga samun kaya Masu quality? Uwar gda Amarya Duk ku tawo 💃🏽 Quality shine takenmu 😻 Muna maraba da masu sayan daya ko sari 👯‍♂️ Muna tura kaya ko ina da yardar Allah cikin Aminci😻 muna zauna a garin Kano cikin kwaryar birni👯‍♂️ masu sayan kayanmu Mina godia👯‍♂️ NA GA RAYUWA…31. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033648387. ★★★ Ina ji Alhaji ya ce “Amma daga yau maganar Miftahu ta kau?” Inna ta ce “Ta kau mana, ba dole ta kau ba tinda kakarsa ta nuna bata so, sai a yi addu’ar Allah ya bata mafiyinsa, ita kuma tata jarrabawar kenan..” Tsawon sati na yi a asibiti kafin a sallameni, saboda likitan ya CE dole a bani kulawa ta musamman don jini na ya hau ka’dan. Ranar da aka sallameni muka koma gida Inna ta dinga kula da ni sosai tana k’ok’arin Kawar min da b’acin ran da nake ciki. Hakan yasa na samu nutsuwa na yi wani fresh tas da ni ba abinda ke damuna sai d’an abinda baa rasa ba. Sai dai wani abu da yasa na tsani zaman garin, sai aka fara yama’di’di da ni har da masu cewa cikin shege na yi a Kano shine aka dawo da ni nan. Abinka da k’aramin gari tuni labari ya kewaye lungu da sak’o aka fara shigowa kallo na. Inna kuwa ba dama ta fita sai a yi ta nunata wannan shi ya tashi hankalin mu da na Inna ta gayawa Alhaji Kano zata mayar da ni, don anan kam duk wanda yazo neman aurena ma gulmar da mutane zasu kai masa ba zai bar shi ya aure ni ba. Alhaji ya jinjina kai ya furta “Sharrin k’aramin gari kenan, mayar da ita d’in shine mafi alheri gaskiya, can birni ba lallai wani ya samu labari ba ma, nan kuwa madadin ta samu nutsuwa sai ta sake firgicewa, amma ki jawa Uwarta kunne ta san irin abinda zata saka ta, don wahalar da take bata ta yi yawa abu sai ka ce a gidan gyaran hali.” Sanda Inna ta gaya min zata mayar da ni Kano ban wani damu ba, don ni kai na zaman garin ya fara isata ba don komai ba sai don kallon da mutane suke min na matsayin Karuwa! Na ha’da y’an kayana na bawa mai aikin Innan don dama ba wasu kaya ne masu yawa ba. Kwana biyu tsakani kuwa muka taho Kano. Inna ta saka Umma a gaba da nasiha akan ta sassauta min, wannan k’uncin da gallazawar ba shi zai gyara ni ba sai ma ya k’ara tab’arb’ara ni, ki nutsu Kubra ki ja y’arki a jiki ki san matsalolinta tun farko ke kika yi saken da kika nesanta kan ki da ita har ta fa’da wannan halin garin kawaicinki na banza da wofi…” Umma ta jijjiga kai murya can k’asa ta furta “In sha Allah Inna.” Shikkenan na samu sassauci har ma na dawo sashen Umman da kwana cikin d’aya d’akinta da bata amfani da shi sai sauke bak’i. Da farin ciki na gyara d’akin na kuma dawo da duk wasu tarkacena da suke sashen Mammy na. Sai ga shi ya fito tas. Daga ranar kuma Umman ta rage hantarata ko saka ni aikin mai wuya. Na so na koma Islamiyya sai dai ban san da wani ido zan kalli Malaman ba. Hakan yasa na hak’ura Umma take biya min karatu tunda ita tayi ilimin addini sosai. Fita ce dai ban isa na fita ko nan da waje ba, hakan yasa na sake wani shegen kyau fata ta tayi fresh sosai. A cikin wannan yanayin aka fara shirye shiryen bikin su Ya.Usman shi da Ya.Umar. Bikin ya rage saura sati guda don haka gaba d’aya hankalin Umma ya koma kan bikin. Nima ina ta shiri na na bayar da d’inkuna na. Umma dai ba wani sake min fuska take ba duk da dai bata gallaza min. Kullum su Yaya Muhammad da matansu sai sun zo gidan jin tsare tsaren biki. Yau ma tun bayan magriba suka zo. in daga cikin d’aki na ji Muryar Anty Khadija tana cewa “Wai Umma AYSHA bata nan ne? Naga kullum idan muka zo ba ma ganinta. Na kuma lek’a d’akin tsakargidan nan ma bata nan.” Ina ji Umma ta yi shiru sai kuma na ji ta ce “Tana cikin d’aki, ni na hanata fitowa cikin mutane tunda dangi suna yawan zuwa bana son ta jawo raina ya b’aci.” Na lumshe ido kawai ina daga cikin d’aki ina sakin murmushi. A.Khadija ta ban ka’da labulai ta shigo, idonta a kaina ina aikin taje gashin da ya bi ya dameni Saboda tsabar yawansa da tsaho. Ga shi na da’de ban yi saloon ba. Baki ta bu’de tana kallona tana dariya “Ah! Lallai AYSHA kin samu kan ki dole ki manta da ni, irin wannan kyau da kika yi haka?” Turo baki na na yi ina furta “Wani kyau kuma? Ni da ko man arziki Umma ta hana ni shafawa ta hanani saka ko kwalli.” A.Khadija ta saki ajiyar zuciya tana karb’ar comb d’in hannuna ta ce “Wallahi kin yi kyau AYSHA fiye da zatonki, ko don dama can ke mai kyau ce..” Ta taje min kan tsaf ta kama ta tufke, sannan ta jawo babbar ledar hannunta “Tashi kiga Kayan bikin da na siya miki.” Ido bu’de nake kallon ha’daddun kayan di’nkuna masu kyau na zamani. Ban san sanda rungumeta da k’arfin gaske ba. Itama dariya ta yi ta rungume ni. Na kwashi kayan na fita da su parlor wajen Umma. Kayan Umma ta Kalla Kafin ta kalli Anty Khadija ta ce “An gode k’warai Khadija, amma da baki wahalar da kanki ba, don Aysha Ba Zata zauna a gidan nan lokacin biki ba… can gidanki ma zan turata su zauna da mai aikin ki da k’anwarki…” Cikin wani irin yanayi nake kallon Umma sai dai bata ba ni fuskar ma da zan mata musu ba, hakan yasa na ja k’afata na koma cikin d’aki, zuciyata ta min rauni na zauna kawai bakin gado na zuba uban tagumi, duk d’okin bikin nan da na ci ashe ma Umma ba zata bar ni na je ba. Anty Khadija ce ta shigo ta zauna kusa da ni. A hankali ta ce “Ki yi hak’uri AYSHA, na san Umma tana dalilin hakan, kada ki ce zaki yi fushi da ita ba Uwar da zata guji d’an ta fa hakan da take miki soyayya ce…” d’aga mata kai kawai na yi ina murmushin da sam bai kai zuciyata ba… Anty Khadija ta min sallama da cewa sai na taho. Na d’aga mata kai. Kashegari jikina a sanyaye na mik’e Umma ta shigo tana kallona “Ki ha’da kayanki, za’a kai ki can gidan Yayanku da yamma.” Na d’aga mata kai kawai. Da yamma kuwa ina zaune a harabar gidan Abba ya saka ni shara don dama haka kawai idan ya bushi iska sai ya ce na fito na share harabar gidanmu. Duk girmanta kuwa haka nake shareta tas, yau ma sharar nake, na ji k’arar shigowar mota, gaba na ya yi wani irin fa’duwa. Tsabar kyan motar ban san sanda na d’aga ido ina kallonta ba, Mai motar bai fito ba kamar yarda nima ban fasa shara ta ba, sai dai ina ji a jikina kallona yake yi. Don haka na ji na bi duk na daburce. Fitowar Yaya Muhammad ne yasa ni ajiye tsintsiyar na zauna a saman wani dakali ina kallon yarda Yaya Muhammad ya nufi inda motar take. Tsawon minti guda na ga an bu’de motar mai Motar ya ziro wasu takalmansa masu kyan gaske, ina d’aga kai na idanuwa na suka fa’da cikin na USTAZU yana tsaye idonsa a kai na… Da sauri na ajiye tsintsiyar ina sakin tsaki na juya na bar wajen… cikin wani irin k’unar zuciya da b’acin rai…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 33… NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Rik’e wajen ya yi da sauri ganin har jini ya fara zuba, amma hakan bai saka shi ya fasa isowa inda nake ba, yana sakin wani kalar murmushi da na rasa fassarar da zan ba shi. Hannu nake ‘d’aga masa ina furuci a zafafe “Don’t come closer Ustaz ka tsaya inda ka ke I hate you…. I hate you whole heartedly….” Murmushin yake kuma bai fasa isa inda nake ba. Na runtse idona zuciyata na wani irin bugu kamar numfashi na zai bar jikina tsabar masifar da take cin zuciyata. Ina ji ya kira sunana da muryar da na kasa yarda tasa ce. “Open your eyes ki kalle ni, ina son mu yi magana…” Ba zan bu’de ba Ustaz, kada ka saka na maka illar da har abada ba zaka manta ba…” na furta da wani irin rawar harshe “Illa?” Ya furta cikin alamar tambaya hakan ya saka ni ware idona a kansa na ce “Ko kana shakka?” Sai naga ya girgiza kai ya lumshe ido ya waresu duka a cikin second d’in da basu fi na k’irga ba… ya ce “Bana mamaki, Saboda komai aka ce za ki aikata yanzu ba zan musa ba, illa kuma ai kin Riga kin gama min illa da kika bari son ki ya Riga ya shiga raina, duk da yanzu ba son ko ka’dan, am just….” Sai naga ya cije leb’ensa ya saki huci ka’dan na ware idona a kansa cikin masifa na ce “You just what? Ka fa’da mana.” “Ina tausayawa Abba da Umma saboda an rasa mai jihadi ya aureki That’s why na yanke shawarar sake aurenki whether you want it or don’t, kawai zan yi manage na aureki….” “Kan Uba!” Na furta cikin tsabar mamaki “Uban waye ya ce na rasa mai so na?” Murmushin ya sake yi ya kuma murza goshinsa ya fice daga ‘dakin yana sake furta “Am not begging you if you wish ki gaya musu ba zaki koma gida na ba, and so what waye ya zama looser….” Ya fita daga d’akin har da y’ar wak’arsa ta larabci. Wasu irin hawaye ne kawai na ji suna zuba a k’unci na zuciyata na wani irin harbawa ina jin kamar na bi Ustaz na kama shi na yi ta duka ko na huta da zafin da zuciya take yi….. Gashin kaina kawai nake ja ina zagin ustaz a fili da zuciyata Samira ta shigo tana kallona kafin ta zauna a gefen gadon ta furta “AYSHA me ye haka, control your self mana, ko kina son wani ciwon ya kama ki nake?” “Na fi so Samira, wallahi ina so saboda ko zai zama Ajalina I hate this world and all the things around it…..” Na fa’da ina sake fincikar gashi na kamar wata mahaukaciya sabon kamu. Ina ji Samira ta ja ni jikinta da k’arfin gaske ta rungume ta fara karanto min addu’oin da suke bakinta. Da k’yar ta samu ta ji na saki ajiyar zuciya ta ja min pillow na kwanta a hankali. Mik’ewa naga ta yi ta fita sai gata ta dawo da magani a hannu. “Tashi AYSHA ki sha magani..” Bu’de idona kawai na yi ina kallonta ta min alama da kai nuni take min tashi na mik’e a hankali ina dafa kai na da yake wani sara min. Na zauna sosai ta saka min maganin a baki ta saka min ruwa, ina runtse idon na ha’diye maganin. Ban farka ba sai sha biyu da rabi na dare. Da sauri na mik’e tunawa da nayi ban yi sallahr Isha ba Samira da take waya ta juyo tana kallona ta kashe wayar. Tana furta “Kin tashi AYSHA?” Na d’aga mata kai kawai na shiga toilet da ke d’akin duk zuciyata ba da’di na d’aura alwala na fito. Ko da na idar da sallah har Samira ta kawo min tea mai zafin gaske da shortbread biscuit. “Ki ci AYSHA na san dare ya yi ba zaki iya cin abinci mai nauyi ba.” Ruwan black tea d’in kawai na d’auka na kai baki na na dinga sipping d’insa kamar magani ina runtse ido na. Samira dai sai kallona take da k’yar na sha Rabin cup na ajiye ina lumshe idona saboda yarda nake jin zuciyata ta yi nauyi kamar wacce aka sakawa dutse. Turo k’ofa muka ji an yi Anty Khadija ce ta shigo idonta a kaina ta ce “Kin tashi AYSHA sannu.” Na d’aga mata kai kawai. Ta zauna da k’yar saboda cikin ta da ya fara girma ka’dan. Ta dafa ni tana furta “Ki daina yawan damuwa AYSHA, kada ki causing ma kan ki wani problem d’in. Samira ta gaya min duk abinda ya faru, abinda nake so da ke ki saka nutsuwa a ranki, ki cire tunanin komai idan Ustaz kome yazo nema ki amince kawai kin…” Wani kallo da na wurga mata ne ya sa ta ha’diye Sauran maganar ta mik’e jikinta a sanyaye tana furta “Shikkenan, Allah ya zab’a mafi alheri.” Ban amsa ba illa mayar da kaina da na yi na sunkuyar. Zuciyata na zafi ni fa gani nake duk wanda zai ce na koma gidan Ustaz baya so na baya k’aunata. Samira ce ta taso ta kama hannuna muka hau gadon ta kwantar da ni. Sai da ta ga na lumshe ido sannan ta ce “AYSHA ki yi hak’uri da abinda zan ce miki, amma wallahi kada ki yi sake Ustaz ya kufce miki, don ya ha’du ta kowane fanni ga kyau ga gayu ga ku’di ga ilimi to me ake so a wajen namiji bayan wannan, ni idan nice wallahi a yau Zan hak’ura a mayar mana da auren tab irin fa mazan nan wahala suke wallahi…” “Tunda kina son sa ke ki aure shi, amma bari na gaya miki wannan karan na shirya fito na fito da duk wanda ya ce sai na komawa auren Ustaz koda kuwa iyaye na ne….” Samira ta ware ido tana kallona. Kafin ta ce “Da gaske AYSHA? Iyayenki fa kika ce?” Lumshe idona kawai na yi ban tanka mata ba, amma a k’asan zuciyata ina gasgata abinda baki na ya furta. Ina kallo Samira ta ja pillow ta kwanta tana furta “Allah ya kau da fitina to.” Sai da aka yi sati ana shan shagalin bikin su Ya Usman, zuwa wannan lokacin kullum Anty Khadija sai ta fita daga gidan kullum Ustaz kuma sai yazo gidan Yaya Muhammad amma koda wasa na k’i yarda ya ganni. Sau d’aya na tab’a hangoshi ta window gefen fuskarsa da plaster da alama inda na ji masa ciwo ne. Na yi tsaki Ina sakin labulen na furta “Ina ma idon na cire maka, mugu kawai!” Anty Khadija da ke baya na ta furta “Da kin cuci y’ay’anki, don dai na san tabbas shine Uban y’ay’anki.” Guntun tsaki na ja kawai na furta “Anty Khadija bana son irin wannan maganar.” Gani na yi ta saki murmushi kawai ta fice daga d’akin. Na bi bayanta da harara saboda yawan zuwansa har na k’agu na koma gidan mu. Don Yaya Muhammad ma duk masifarsa ya gaji ya k’yaleni ganin ba zan tab’a saduda ba. A daren ranar da na kwana goma a gidan Yaya Muhammad ina kwance d’akin da nake Ayra a gefena sai surutu take. Anty Khadija kuma tana parlorn Yaya Muhammad. Turo k’ofa na ji an yi ina d’aga ido na ga Yaya Muhammad ne kafin na gyara kwanciyata ya matsa yana kallon Ustaz ya ce shigo gata nan.” Da sauri na mik’e ina gyara mayafin abayar da ke jikina. Na b’ata fuska sosai kamar ban tab’a dariya ba. Gefen drawerr na kalla sai naga yajin da naci waina yana nan. Murmushi na saki a raina na ce yau zaka san baka da zuciya. Yaya Muhammad ya juya hannunsa d’auke da Ayra tana yiwa Ustaz gwarancin da alama har ta saba da shi. Ina gani ya mik’a mata Bounty chocolate sai naga ta saki dariya suka fita da Daddyn ta. Zama ya yi a kujera k’waya d’aya da take d’akin ya d’ora k’afa d’aya kan d’aya yana k’are min kallo. “Mara kunya…” ya furta cikin wata murya mai bayyana k’asaitarsa. Muryata a dake na ce “Ka tashi ka fita!” “Idan na k’i fa? Me zaki min?” Wani murmushi na saki ina gyara zama na na ce “Zai fi maka sauk’i ka tashi ka fita wallahi, kafin an aiwatar da abinda na shirya…” shiru ya yi bai fitan ba sai dai ya kafa min ido yana cije leb’ensa ya ce “Gaisuwar ma kin manta yarda ake yin ta?” Na zo fa iya wuya don haka na kasa amsa masa, sai furzar da huci nake. “Ba kya ji ne AYSHA?” Jijjiga k’afata nake yi kawai zuciyata na ayyana min na watsa masa yajin kawai. “Ki sassautawa zuciyarki AYSHA ki nutsu magana nazo mu yi ba tashin hankali ba..”. “Ba zan sassauta ba Malam, bari na gaya maka kada banzar zuciyarka ta fara Kimtsa maka ka mayar da aure na, wallahi zaka yi nadamar hakan matuk’ar nadama…” cikin mamaki Ustaz yake kallo na ni kuwa na masa funfurun fus sai masifa nake masa. Bai yi min magana ba naga ya mik’e ya fita k’ofa jikinsa a sanyaye, na zabga tsaki ina tashi na rufe k’ofar har da murd’a key. Sai sannan wasu hawaye masu zafi suka zubo min. Na zauna kawai ina dafa k’irjina da naji ya matsanta min da bugu. Kwana biyu sosai na ‘d’au fushi da mutanen gidan. Bana kula kowa sai ta kama. Kowa ma haushinsa nake ji. Yau na tashi da wuri na yi wanka ban yi wani kwalliya ba illa powder da lipgloss da na saka. A parlor na ga mutanen gidan suna karyawa. Yaya Muhammad yana gani na ya wani saki murmushi na lura tunda Ustaz ya dawo yana musu nacin a mayar da aurena da shi yake sakar min fuska. Yanzu ma cike da walwala ya furta “Ayshatu Gaye kin tashi?” Tsuke fuskata na yi na furta “Ina kwana?” Kamar bana so. Ya amsa ba tare da ya damu da fisgar da nake masa ba. Ki zo ki karya, zan kai ku gaba d’aya can gida ku wuni.” Tab’e baki na na yi na ce “Ina azimi…” Ya juyo yana kallona ya ce “Azimin me kuma AYSHA naga yau Talata…” Shiru na masa har sai da ya sake tambayata sannan na ce “Azimin kada Allah ya bawa Ustaz da duk wani mugu sa’a akan mayar da aure na da shi…” Sak naga ya yi cup d’in tea d’in a hannunsa yana kallona ko k’iftawa ba ya yi. Ni kuwa ban damu ba na ‘d’auke kaina daga kallonsa sai ta k’asan ido na dinga kallonsa sai can na ji ya yi k’wafa ya ce “Ni da iyayenki mu ne mugayen kenan?” Ban amsa masa ba na mik’e zan bar wajen ya yi saurin fisgo ni na dawo gabansa na durk’ushe. Sai kuma na ga ya sake ni yana murmushi kawai ya mik’e kin ci sa’a na yiwa Ustaz alk’awarin ba Zan sake kai hannuna jikinki ba, Allah da yau kin sha mamaki, tashi a nan mara kunya kawai don ma kin ga ana lallab’aki, kuma aure kamar kin koma gidan Ustaz kin gama…” “Sai dai idan ni Ayra ce… amma wallahi ba zan koma ba…” wannan karan har Anty Khadija kallo na take da mamaki fal fuskarta ta ce “Ayshatu are you out of your mind…” Ya sake ni bayan ya yi blowing wani zazzafan huci ya zari car keys d’insa ya ce “Khadija maza ku fito mu je can gidan, yau za’a yi ta ta k’are dama duk Ustaz ne ya ja da har ya ce wani a lallab’ata ga shi nan tana niyyar yiwa mutane rashin kunya, yau zaki san nima ina iko da ke kamar yarda nake iko da Ayran…” Ya fa’da idanunsa fici fici cike da zallar masifa. Ban wani damu ba na mik’e na zura hijabi na a zuciya nake furta “Mu je gidan mana sai me wallahi ko me za’a yi ba zan koma gidan wancan wawan mutumin ba…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 34…. MIKIYA WRITERS🕊. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ Ba wanda ya bi ta kaina a cikinsu, hirarsu suke a cikin mota fuskokinsu cike da nisha’di. Hakan ya sake dugunzuma zuciyata ganin da gaske basu damu da damuwata. Ita kanta Anty Khadyn sai na fara jin haushinta. Har muka isa gida huci kawai nake zubawa na tsabar turirin da yake zuciyata. Fuskata a d’aure tamau na shiga gidan ina yi ina ciccije baki don ma a san duk abinda zan fa’da d’in har k’asan zuciyata haka yake. Abba da Umma muka tarar a zaune suna ta kallon kayan garar Yaya Usman da aka kawo. Ko kallon kayan ban yi ba na mik’e zan shige parlorn Umma na k’asa. Abba ya saka baki ya kira ni, kiran da naji har tsakiyar kai na. Ba don komai ba sai don mamakin yanayin yarda ya yi kiran a tausashe cikin nutsuwa kamar dai Abba na na wancan lokacin kafin komai ya juye. Cak na tsaya ba tare da na juyo ba. “Ki zo na ce Ayshatu..” Ya sake furtawa. Na juya na koma na zauna ina jingina da kujera idona a lumshe. Bai min magana ba suka cigaba da tattaunawar da suke akan yarda za’a raba ma dangi kayan garar. Sai da ya gama tas sannan ya juyo yana kallona ya ce “AYSHA! D’ago ki kalleni.” Na yi saurin d’aga ido ina kallonsa, zuciyata na wani irin bugu don na san tabbas ba mamaki maganar Ustaz zai min. “Waye ni?” Tambayar ta min wani banbarakwai don haka na rasa amsar da zan ba shi, “Ki gaya min waye ni na ce miki? Matsayin me nake a wajenki?” Sai yanzu na gane tambayar tasa. Muryata cike da rauni na amsa masa da “Kai Mahaifina ne…” Ya girgiza kai yana furta “Madalla da kika fahimci haka, kin san ina da iko da ke ko? Musulunci ya bani damar na baki umarni kuma ki yi min biyayya dole matuk’ar ban kaice hanya ba ko? Sab’anin hakan kin san hukuncinki a wajen Ubangiji ko?” Madadin amsa masa lumshe ido na na yi kafin naji wasu tarin hawaye suna zubo min. “Ki amsa min mana? Kin san wajibi ne biyayya ga iyaye ba sunna ko mustahabbi ba?” Na ‘d’aga kai kawai sai naga ya girgiza kai “amsa ta fatar baki Aysha..” murya cike da rauni na ce “Na sani Abba.” Yauwa a yanzu zan gaya miki ni mahaifinki Imam Khalil na yarjewa Ahmad Sulaiman sa’eed aurenki a karo na biyu, a yau da daddare zan karb’i sadakin ki a d’aura auren….” Zuciyata na ji ta yi wani irin matsanancin bugu, na dinga ware ido ina kallon Abba cikin kakkarwar murya na ce “Wallahi Abba bana son sa….” bayan haka ban sake sanin inda kai na yake ba, sai farka wa nayi na ganni saman gadon Umma gefe guda Umma ke zaune hannunta rik’e da nawa an saka min drip. Na bu’de idona sosai maganganun d’azu suna dawo min ina fatan duk abinda ya Farun ya zama mafarki ba zahirin gaskiya ba. Shigowar Yaya Usman ce ta saka ni sakin ajiyar zuciya, sai a sannan Umma ta san na farka ta juyo da sauri tana kallona ta ce “Aysha kin farka?” Na d’aga kai na a hankali ina jin kan yana wani sara min. Na ce “Umma zan sha ruwa…” Sai naga ta mik’e da sauri tana furta bari na kira likitan na ji ko za’a iya baki ruwan..” Yaya Usman ne ya matso inda nake, idanunsa cikin nawa kafin ya zauna a saman drawerr da take gefen gadon. Murya k’asa ya ce “Sannu Aysha Gayu, me yasa kike son sakawa kanki damuwar da take neman haddasa miki ciwon zuciya, kina son ki mutu ne?” Da sauri na d’aga masa kai. Sai naga ya bu’de ido ya ce “Why?Aysha sai kace ba musulma ba? Duk musulmin k’warai fa ya kamata ya yarda da k’addara mai kyau ko marar kyau, me ye aibun Ustaz a duk abinda nan da ya faru da ba kya son ki koma gidansa. Duk namijin da hakan ta faru a kansa fa abinda zai aikata kenan, ko nine a shoe d’insa zan aikata fiye da hakan ba tare da wani bincike ba, kin san yarda kishin maza yake kuwa, change your mind AYSHA Ustaz Shine Mijin da ya dace da ke, pls kada ki sake hurting zuciyar su Abba a karo na biyu. Ki kawar da zugar da shai’dan yake miki akan ki bijirewa umarnin iyayenki hakan ba zai zama alheri a gareki ba, biyayya ga Abba da abinda yake so sai kiga kin dace fiddunya wal Akheera..” Runtse idona na yi da k’arfin gaske, jin abinda Yaya Usman ya ce, idan har na fahimcesa so yake lallai na koma gidan Ustaz don yin biyayya ga Abba, amma ina sai nake jin zuciyata ba zata iya d’aukar nauyin k’addarar komawa gidan Ustaz ba. Ya kama hannuna ya matsa a hankali. “Ustaz yana son ki Aysha fiye da tunaninki, banda yana sonki ba abinda zai dawo da shi neman aurenki a karo ba biyu…” Hannuna na zare ina share hawayen ido na na ce “Baya sona Yaya Usi yaudara ce kawai, wallahi baya sona da abinda ya saka ya dawo neman aurena ne don kawai ya tozarta ni ya kuma cimma wata manufa tasa.” Dariya Yaya Usman ya yi ya ce “wallahi yana sonki fiye da zatonki, tunda abin nan ya faru bai sake samun kwanciyar hankali ba, kada ki sake saka shi a tunanin baki da kunya ba kuma kya biyayya da iyayenki, ki min alk’awarin za ki yi hak’uri….” na lumshe ido na kawai ba tare da nace masa komai ba. Shigowar Umma ce tasa ya mik’e yana shafa kumatu na ya ce “Be a good girl dear, bari na je sai da safe Umma.” Umma ta ‘daga kai tana ce masa Sai da safe Usman ka gaida Husna. Ya amsa yana d’aga min hannu, da murmushi fal a fuskarsa. Ban mayar masa don bani da sukunin murmushin zuciyata nake jin kamar ana hura min wuta a cikinta. Magani Umma ta sake bani, bayan na sha tea na yi sallahr Isha’i wani barcin ne ya sake d’auke ni. Abin mamaki ban tashi farka wa ba sai da Umma ta tashe ni sallar asuba. Ina ji a cikin maganin da aka bani har da na barci tsaf na tashi kaina baya ciwon da yake min, sai dai d’an jiri da nake ji na rashin cin abinci. Sai da na idar da sallah Umma ta dubeni tana amsa gaisuwata ta ce “Abbanki yana buk’atar jin shawarar da kika yanke, akan komanki gidan Ahmad, ni dai idan har zan baki shawara ki d’auka a matsayina na wacce ta kawo ki duniya zan ce miki ki koma gidan Ahmad, ba don komai ba sai don na san zai rik’eki da mutunci, na yi mamaki ma da ya dawo neman komawa aurenki duk da abubuwan da suka faru. Saboda haka ina jin ki don jiya da zasu kawo sadaki ma ya ce a bari a ji ta bakin ki… shin kin amince?” Wani irin runtse ido na yi ina cije leb’ena da k’arfin gaske kamar zan huda su, ina ji a raina bana son Ahmad amma kuma yana yak’i da zuciyar da take son saka ni bujirewa umarnin su Abba, Nasihar Ya Usi tana ta dawo min a zuciyata. Muryar a dake na ce “Na amince..” Sai naga Umma ta saki ajiyar zuciya ta saki murmushi ka’dan ta ce “Allah ya miki albarka, yasa a ce gwara da aka yi. Alhamdulillah Allah ya k’ara shiryaki ya shirya dukkan lamarinki.” Ta mik’e ta fita cikin walwala da farin ciki ni kuma ta bar tawa zuciyar cikin matsanancin k’unci da b’acin rai, ina jin yarda yanayin bugun zuciyar tawa yake sauyawa na lumshe ido ina ji a raina na amince zan koma gidan Ustaz ba don komai ba sai don na wanke kai na daga zargin da yake min, daga ranar kuwa da ya kusanceni ya ji ni a matsayin budurwa wallahi daga ranar zan b’alle kayan yak’i na har sai ya gwammaci ki’da da karatu. Sai kawai na saki murmushi ina gyara kwanciyata. Har a zuciyata ina jin shawarar ta yi min daidai yarda nake so. Daga ranar da na amince da auren Ustaz shikkenan na samu sakin fuska sosai daga wajen mutanen gidanmu. Ciki kuwa har da Abba aka karb’i sadaki na a karo na biyu daga iyayen Ustaz. Gefe guda ni ka’dai na san wutar da zuciyata take kunna min akan lamarin auren. Aka sake d’aura aurena da Ustaz ba tare da na sake bari ya ganni ba. Shima tunda ya zo sau d’aya na fita na mak’ale a waje ban je wajensa ba bai sake dawowa ba. Na tattara lamarinsa na watsar na dinga tunanin kalar ramuwar gayyar da zan masa. Da daddare ina zaune a d’aki Umma ta shigo tana kallo na ta ce “Gobe ki fara zuwa gyaran jiki AYSHA kin ga zuwa nan da kwana biyar za ki tare.” D’aga mata kai na yi kawai. Ta kawo wani cup cike da madara kindirmo da magani da na tabbatar na mata ne a ciki ta bani. Godiya na yi na karb’a ina sha. Idan kin gama Aysha ga turaren tsuguno nan ki zuba a garwashi ki yi.” Na d’aga mata kai kawai. Don abinda zata bani bana k’in amfani da shi don na san amfaninsu kuma da wannan damar nake son Jan Ustaz a k’asa har sai ya gane shayi ruwa ne don na yi alk’awarin auren d’and’ani haukaci Zan masa, nemana zai yi ya rasa ko na maka shi kotu ya sake ni. Bayan fitar ta da 1 hour sai gata ta shigo. “Aysha Ki je ga Ustaz can a falon Abbanki…” Zuciya ta naji ta hassalo wato don ya san bana zuwa wajensa shine yau ya shigo har Parlorn Abba. Na tsuke fuskata kafin na yafa mayafin doguwar rigar da take jikina raina a b’ace na shiga d’akin ko sallama ban masa ba… Gani na yi ya mik’e tsam ya iso inda nake yana wani sakin murmushi. Na juya zan tafi na ji ya fisgo ni da k’arfin gaske na fa’da jikinsa. Ture shi nake da k’arfin gaske amma bai bani damar kub’uta ba, kawai na ji tattausan lips d’insa a saman nawa. Sai da tsotsa son ransa sannan ya janye jikinsa yana zama saman kujera hannayensa a cikin gashin kansa yana burkita gashin, idanunsa a lumshe. Takaici ya isheni a zafafe na ce “Allah ya isa kissing d’ina da ka yi, mugu kawai!” Ya ware birkitattun idonsa a kai na sai naga ya saki murmushi ya ce “Me ye a cikin lips d’in naki? Leb’e da k’arti suka gama tsotsewa kin zata lallab’a ki zan yi, ki shirya duk ranar da kika shigo gidana sai na fanshe wahalar da kika ba ni, kafin nan ki shiga ki saka hijabs zan kai ki gwajin H.I.V….” Cak na ji zuciyata ta tsaya da bugun da take idona da kunnena kuwa kamar basa aikin da ya kamata idanuna a burkice na nuna shi da yatsa bakina na rawa na furta “In dai kai d’an halak ne Ustaz ka sake saki na yanzun nan a karo na biyu, bana son ka ba tsaneka kuma ba zan tab’a komawa gidanka ba Ahmad ko kai ne Autan Maza! 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ 08033748387. [10/16, 5:43 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 32. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Ban san me ya ce da Yaya Muhammad na dai ji Ya.Muhd ya ce “Ke Aysha!” na juyo fuskata a masifar d’aure “Ba zaki gaishe shi ba?” daga shi har Ya.Muhd d’in na musu wani banzan kallo na sake juyawa na yi wucewata cikin gida idanuwa na suna shirin zubar da hawaye. Ban bar ko Umma ta ganni ba na yiwa kaina masauki a cikin d’akina ina mayar da huci idona a runtse nake tunanin Uban me ya kawo Ustaz kuma gidan mu? Shin akwai sauran alak’a ne a tsakaninsa da gidan mu? Ban dawo daga tunanin da nake ba na ji Yaa Muhammad yana tambayar ina nake? Ina ji Umma ta ce tana cikin d’aki, wani abin ta yi ne na ga kana ta b’ata rai…” muryarsa cike da takaici ya furta “Kin ga kallon banzan da ta yiwa Ahmad, kamar wata mara hankali…” bai saurari Umma ba ya bugo door d’in d’akin da wani irin k’arfin gaske. Idanunsa a kai na yake zuba wani irin kallo, kafin ya k’arasa cikin d’akin fisgo ni ya yi da k’arfin gaske yana min kallon cikin k’wayar ido… “Wa kika gani kika wulak’anta, kina da hankali kuwa, are you out of your senses da ina maki magana zaki kalleni with your shameless eyes ki juya ki tafi…” Turo baki na na yi don kam wallahi sai dai ya kashe ni idan akan wancan mutumin ne da ko sunansa bana son na dinga ji a rayuwa ta. “Kin zata zuwa ya yi biko da kika nemi ki disgracing d’insa?” Sai na ga ya ciji bakinsa ya furta “Ba biko yazo ba, at all ma ba wajenki ya zo ba yazo kawowa su Usman gudumawar biki ne marar kunya har kika nemi wulak’anta shi…me zai yi da ke?” “Nima me Zan Yi da shi ko maza sun k’are ba zan sake kallonsa a matsayin masoyi ba sai dai gagarumin mak’iyi.” Ya.Muhd tsayawa ya yi yana kallona with a lot of surprises a kan fuskarsa sai na ga ya yi dariya kawai ya furta “Rubbish!” Ya fice daga d’akin. Ina ji yana sake bawa Umma labari, Umma bata ce komai ba ta ce Allah ya kyauta. Da daddare sai ga Yaya Usman ya shigo d’akin da nake da fara’a fal fuskarsa ya zauna a gefen gado yana kallo na. “AYSHA ya naga mood d’inki ya canja?” Sai sannan na samu hawayen da yake idona ya fara suntiri na fara basa labarin abinda ya faru. Madadin ya ji haushi sai naga ya yi murmushi ya ce “AYSHA Ustaz fa bai cancanci haka a wajenki ba, kada kiga ya banzagatar da lamarinki kullum wallahi a cikin maganarki ya ke, har group muka ha’da na whatsapp da shi da y’an mazan gidan nan duk akan matsalarki muna so mu gano menene zahirin gaskiya, sannan da saka hannun Maminki a ciki ko bab…” Kallon da na masa ne ya saka shi jan bakinsa ya yi shiru yana dariya k’asa k’asa ya ce “Idan biko yazo Ai sai a ha’da da namu kawai a d’aura ki koma gidansa shikkenan baki alaikum…” Da sauri na ce “Ashe kuwa za’a kai Gawata gidan Ustaz don wallahi tsaf zan kashe kai na…” Ya.Usman waro ido ya yi ya ce “To Allah ya rufa asiri, yanzu ma fa zuwa na yi na gaya miki kyautar motoci ya kawo mana masu masifar kyau ni da Umar matsayin gudumawarsa da zunzurutun ku’di…..” Da sauri na saka hannu na na rufe masa bakinsa, ina girgiza kai na ce “Ya.Usman don Allah tashi ka fita, bana son jin komai….” Na fa’da idona a runtse ina zubar da wasu zafafan hawaye. Shiru Ya.Usman ya yi kafin ya mik’e jikinsa a sanyaye yana furta “Take heart AYSHA ba wai nufi na ki koma gidan Ustaz ba…” Ban bi ta kansa ba na mik’e a guje na koma cikin toilet ina mayar da wani irin nauyayyan haki. Kwana biyar tsakani Umma ta ce na tattara kaya na na koma gidan Ya.Muhd kada na dawo har sai an gama biki. Idona cike da hawaye na ce “Umma ba zan yi attending bikin ba?” Ba zaki yi ba Aysha, akan me za ki yi attending biki? Idan yaso duka idanun y’an biki ya dawo kan ki da wanda ya san labari da wanda bai sani ba kowa ya ji ko?” Na girgiza kai na. Tsam na mik’e na fara tattara kaya na zuciyata a mugun k’untace. Ina gamawa Umma ta ce na fita driver na jira na. Da sauri na fita idona na zubar da k’walla. Umma ta d’an yi tsaki kawai. Ina ji tana furta “Sai na zauna ina kallo mutane suna nuna ki ana yama’didi da abinda ya faru saboda ba ni da kai, bakin duniya ya je ya sake tagayyara ki.” A mota ba abinda nake sai tsinewa mutumin da ya yi silar shigata cikin wannan matsalar da ban ji ba ban gani ba. A gidan Yaya Muhammad kuwa da wani irin murna da farin ciki su Anty Khadija suka tare ni. Ga k’annenta har biyu da ta kawo su taya ni zama. Ayra y’ar su y’ar shekara biyu itama ta ‘dafe ni tana dariya. Sai na ji duk wani k’uncin zuciyata ya fara Yayewa na rungume Ayra ina dariya. Wanka na shiga na fara yi, don yinin yau kaf ban yi wanka ba. Kai na da yake cunkushe Anty Khadija ta kalla ta yi tsaki tana furta “Sannu Aysha, so kike ki lallata gashin ki ko? Maza Samira shirya ki kai ta saloon d’in da muka je jiya a gyara mata kai, a mata predicure da manicure, kada ku dawo gidan nan sai na ganta tsaf kamar amarya.” Na turo baki na ina furta “Ki bari sai gobe Anty Khadija daga zuwa na, ni fa duk wa’dannna abubuwan yanzu bana son su..” Khadija ta tab’e baki ta ce “Yanzu kuwa zaku tafi, kuma har lalle sai an miki duk da dai ba ke za’a bikin.” Girgiza kai na yi na ce “Gaskiya zan yi komai amma banda lalle.” Anty Khadija bata kula ni ba ta bawa Samira Atm ta ce “Idan kun dawo a d’aura girki ni zan je wajen Umma.” Na fita ina jan hannun Ayra da ta bi ta mak’ale min. Samira k’anwar Anty Khadija tunda muka fita take aikin yi min nasiha, da nuna min illolin bin ru’din samarin Zamani. Kallonta kawai nake ina mamakin kalamanta ban ce mata komai ba illa murmushin takaicin da nake saki, don na san ba laifinta ba ne, kowa kallon da yake min kenan. Tsaf aka wanke ni aka gurji fatar jikina duk wani datti da ya mak’ale min sai da ya fita tas jikina ya zama kamar mudubi tsabar santsi da sulb’i. Gashi na ya yi tsaho na ban mamaki. Ni kaina da na kalli kai na a mudubi sai da na sake kallon kai na na saki murmushi. Mai gyaran kuwa sai cewa take “Ma sha Allah! Wannan in dai amaryace yau na san zautarwar da zaki yiwa mai gidan Allah ne ka’dai zai k’wace ku, irin ku ko fatar jikinku ba zata bari a yi kishi da ku ba, jiki kamar tarwa’da.” Murmushi kawai na saki. Ina jin yarda jikina yake wani tashin k’amshin turaren da aka min na jiki. Muka biyata ku’dinta muka fita Samira ma sai zuzuta kyan da na yi take. Girki muka d’ora don Anty Khadija ta ce mu ‘dora girkin Ya.Muhammad yana azimi kasancewar alhamis ce. A gurguje muke aikin don lokaci ya Riga ya k’ure. Kunun kwakwa da madara muka masa sai plantain da chips da liver sauce. Muka ha’da masa tamarind juice da aka ha’da da apples. Ganin mun gama na tattara ba barwa Sameera gyaran kitchen d’in. Na ja hannun Ayra don na mata wanka don duk ta b’ata jikinta da cornflakes d’in da ta sha. Duk toilets d’in bedrooms d’in ba ruwan zafi ya k’are haka yasa na janyo hannunta zuwa na sitroom da Samira ta ce min akwai ruwan wankan. Anan na mata wankan ban san da mutane a parlorn ba hakan yasa na ajiye hijab d’ina na fito gashi na kwance a saman baya na jikina kuwa wata Riga ce k’arama na fito rungume da Ayra a hannuna. K’iris ya rage na saki Ayra a k’asa ganin wa’danda suke zaune a sitroom d’in. Ya.Muhammad ne da Ustaz da wani da ban san sunansa ba. Kuma mutumin ya kafa min ido kamar zai ce babu. Ta k’asan ido nake kallon yarda fuskar Ustaz ta yi kicin kicin da b’acin rai. Na rasa yarda zan yi tabbas idan na fita a haka ba abinda ba zasu gani ba a jikina, don Rigar irin tsukakkiyar nan ce da ta fitar da duk wata sura a jikina idan na ce har Shatin pant d’ina ana gani ban yi k’arya ba. Idan har na juya zuwa toilet d’auko Hijab d’ina nan ma za su ga baya na. Ya Muhammad ya mik’e don da alama bai lura da ni ba. Sai na ga Ustaz ya mik’e ya nufo inda nake fuskarsa a mugun ha’de ya wani irin zabga min kallo ya yi bake-bake a gaba na ta yarda na zaunen ba zai iya gani na ba murya a cunkushe ya ce “Koma cikin toilet Malama!” Da wani irin sauri na shige cikin toilet d’in don dama irin taimakon da nake so kenan. Na d’au Hijabi na da yazo min har k’asa na fice a toilet d’in kai na a k’asa. Ina ji Bak’on ya furta “Ahmad wacece wannan d’in.” Murya can k’asa na ji Ustaz ya furta “My Ex-Wife…akwai wani abu ne?” Ni dai na shige ciki da sauri duk jikina b’ari yake na dinga ja musu Allah ya isa kamar laifina ne ba nasu ba. Tunda na shiga kuma ban fito ba. Sai da Sameera ta lek’o d’akin tana kallona ta ce “AYSHA ki je in ji Abban Ayra kina da bak’o.” Baki sake nake kallonta kafin na furta “Bala’i, ki je kice ba zan zo ba, nazo na masa Uban me?” “Ki masa Ubanki, mara kunya fitsararriya…” na samu muryar Ya Muhammad yana furtawa a sama. “Ba zaki tashi ba..” Da wani irin k’arfin hali na ce “Wallahi na zani ba…” Sai naga Yaya Muhammad ya bu’de ido ni kuwa na cigaba da cewa “Ai wallahi ko kashe ni zaka yi ba zani ba…” Ban yi aune ba naji saukar mari a saman fuskata a zafafe Ya.Muhammad yake furta “Ni kike gayawa haka, da kika samu har yazo yana son ganinki banda shima baida zuciya ban ga Uban da yasa zai sake neman aurenki ba a karo na biyu.” Duk da zafin marin da na ji bai hana ni sakin wani murmushi ba na ce “Na rantse da rabbu ba zan je ba Yaya Muhammad sai dai kai gutsi gutsi da nama na, da na koma gidan wancan mutumin gwara na mutu ba aure…” Zai sake kai min duka sai naga Sameerah ta hana hakan yasa ya fice a hassale yana fa’din Samira fito bari na saka shi ya shigo cikin d’akin tunda ita bata da mutunci. Ina kallo Samira ta fita na wani irin dariya ina wawurar wani sandan labulai da yake gefe na na tsaya a tsaye kamar y’ar Caburos so nake kawai Ustaz ya shigo na tafka masa. Zuciyata tana wani irin zafi na ji an turo k’ofar yana sallama cikin kwantacciyar murya. Ko rufe bakinsa bai yi ba na cilla masa sandar ina huci na nuna shi da yatsa….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 35…. NAZEEFAH SABO NASHE.★✍️ 08033748387. Kallona Kawai yake Yana sakin murmushi a hankali kafin cikin sanyin murya ya ce “Idan suka mayar da ke gidan nawa ki fita kin Ji Aysha.” Daga haka ya fice daga cikin sitroom d’in. Ji nayi kamar ana hura wuta a cikin zuciyata na runtse ido kafin na kwarma wani Uban ihu da yaja hankalin mutanen gidan suka shigo inda nake a guje. Umma ta k’araso tana kamani cikin rawar murya ta ce “Ke menene? Me aka miki?” Ban fasa kukan ba ina kallon k’wayar idonta data bayyana tashin hankalin da take ciki. Na ce “Umma ku yi min rai wallahi Ustaz ba don Allah ya dawo na koma gidan da ba, akwai wani kalar mugunta a ransa wanda Allah ne ka’dai ya sani.” Shiru Umma ta yi kafin ta kama hannuna ta d’aga ta ce “Mu je cikin gida, naji me ya ce miki.” Bin ta kawai nake ina sake kukan da nake. A d’akinta ta saka ni kafin ta ja k’ofa ta rufe. Ta dawo inda nake bakin gado ta zauna ta ce “Oya gaya min, me ya ce miki?” Tsaf na gaya mata abinda ya ce min, sai naga ta yi shiru tana girgiza kai, ta saka hannu ta share min hawayen fuskata ta ce “Ki yi shiru Aysha, a dole dama zaki fuskanci irin wannan matsalar daga wajen duk Mijin da zai aureki.” Ta yi shiru tana share k’wallar idonta kafin ta ja hannuna ta matse a hankali da alama duk abinda take son ya fito daga bakinta mai ciwo ne a zuciya… “Duk macen da ta rasa budurcinta a yawon banza AYSHA dole ne ta fuskanci irin wannan k’alubalen a wajen Mijin da zata aura, don haka dole ki jajirce wa ranki kika saka ranki bautar Ubangiji zaki yi ba bautar Ustaz ba, to shine zaki samu salama!” Hawaye ne masu zafi suka zubo min a hankali na ce “Ni fa Umma ban rasa budurci na ba, kuma wallahi babu wani namiji da ya tab’a rik’e min hannu bayan Ustaz to me yasa zaku yi ta jefa zargi na a zuciyarku…shiru fa kawai nake muku ni ban aikata abinda ake zargi na ba, ku yi bincikien mana ku gani…” K’wayar idonta kawai take zagayawa cikin tawa tana kallo na ta ce “A yau d’aya na yarda da ke Aysha don ban hango k’arya a cikin idonki ba, amma abinda na kasa ganewa how comes duk wa’dannan abubuwan suke faruwa, bincike kuma wallahi ana yi daga Abbanki har y’anuwanki da shi kansa Ustaz d’in tunda abin ya faru har yau basu huta ba, k’arshen lamarin ne kawai bai zo ba….Allah ka dube mu ya Allah, Allah yasa kuma abinda kika fa’da hakan yake. Yanzu ki share maganarsa idan kin je gidansa ya tara da ke ya sameki a matsayin cikakkar budurwa anan lamarin zai canja.” Shiru na mata ina sakin ajiyar zuciya “Kin ji me na ce miki ko?” Na ‘d’aga mata kaina yau d’aya sai naji wani sashe na k’uncin zuciyata yana zagwanyewa. Ta mik’e ta fice cikin matuk’ar sanyin jiki. Shirye shirye sosai ya kankama duk na komawata gidan Ustaz. Duk wani gyara Umma ta min ta saka kuma an ha’da min wasu shegun kayan gyara daga wajen Maman Fareeda mai kayan gyaran aure. Ni da kaina ina jin yarda jikina ya sauya. Wani irin glowing nake na yi kyau ba ka’dan ba. Ustaz ne dai ban sake saka shi a idona ba tun bayan da ya gama gaya min bak’ar maganar da har yau ta kasa barin zuciyata na kuma rik’e a raina da cewa sai na rama wallahi ko ba yanzu ba. Tsaf aka shirya ni cikin wata zafafffuyar laffaya da ya sha k’amshin turaren gabbasa, duk inda na wuce k’amshi ne, hatta da gashi na baa k’yaleshi ba sai da aka turarashi jikina fa kamar an min b’arin madarar turare. Umma kuwa kana kallon fuskarta zaka san tana cikin tsananin farin ciki. K’arfe takwas Abba yasa aka kai ni cikin motarsa don da kansa ya ce zai kai ni gidan Ustaz d’in. Tun a mota yake min nasiha bai fasa fa’din. “Bana son a k’ara samunki da wani laifin AYSHA,ki tabbata kin rik’e mijinki da girma da mutunci kamar yarda mahaifiyarki take min.” D’aga kai kawai nake idona bai fasa zubar da k’wallar da take kwarara ba. Har cikin parlor ya kai ni ya zaunar saman Kujera Ustaz da ya shigo da mu ya durk’ushe a gefensa ba yarda Abba bai yi ba ya zauna a saman kujerar ya k’i. Nasiha ya masa sosai a k’arshe ya ce “Ga amana nan Ustaz na baka Allah Ubangiji ya baku zaman lafiya ya kawar da dukkan abin k’i. Waccan magana kuma da muka yi da kai kada ka fasa ka cika umarnin da iyaye suka baka, Allah ya baku zaman lafiya.” Ustaz ya amsa da ameeen. Abba ya mik’e ina kallo ta cikin mayafi Ustaz ya mik’e don raka shi. Na runtse ido ina jin wutar tsanarsa da jin haushinsa yana sake nuk’urk’usar zuciyata. Na yaye mayafin laffayar fuskata ina k’arewa tangamemen parlorn da ya sha kayan alatu kallo. Sam ba abinda ya burge ni a parlorn don ba abinda nake so ba kenan. Wancan Karon an shigo ni da ni gidansa da tsananin son sa wannan karan kuma na shigo da tsananin k’iyayyarsa a zuciyata. Jin takun shigowar sa parlorn na sake Kimtsa fuskata ina hura hanci cikin tsananin fushi. K’arasowa ya yi cikin parlorn ya kuma zauna a kujerar da nake kai. Ina kallo ya jingina yana lumshe ido, kafin naji ya fisgo ni da k’arfin gaske na fa’da jikinsa gaba d’aya ya rungumeni yana sakin ajiyar zuciya a kai a kai. Da sauri nayi k’ok’arin k’wace kai na sai dai bai bani damar hakan ba, ya sake rungumeni sosai idonsa a lumshe ya saka lips d’insa akan nawa yana tsotsa hankalinsa kwance k’ok’arin ture shi nake amma bai bani dama ba a kunne ya ce “Shsssh! Bar ni na Mori sadaki na Malama, naga dai ni na biya wani banza ma….” Sai naga ya yi shiru ya runtse ido a hankali kuma ya fara sassauta rik’on da ya min kafin ya sake ni gaba d’aya ya mayar da kansa jikin kujerar idonsa a lumshe, mik’ewa na yi da niyyar na masa rashin mutunci sai naga idanunsa na zubar da hawaye duk da a lumshen suke k’irjinsa yana sama da k’asa. Hannuna ya ja kafin ya bu’de idonsa a kaina da suka ka’da suka yi jajir. Mamaki ya bani ganin kuka yake sosai. Kallona yake yana murza hannuna yana hawayen still cikin wata irin murya ya ce “Why Aysha? Don Allah wanene wannan mutumin da kika…” naga ya runtse idonsa yana jijjiga kai ya furta “Allah ya isa ya cuce ni, wallahi Aysha ya min illa a zuciyata. Gashi zuciyata ta kasa amincewa na bar ki, me yasa Aysha don Allah?” Tsuke fuskata na yi ina jin wani irin takaici a raina da mamakin kukan da Ustaz yake yi. “Har kika iya sallamawa k’ato jikinki hannunsa a saman abinda nafi so yana latsa su son ransa, na rantse duk ranar da ya bari na yi ido biyu da shi sai na kusa hallaka shi kafin na ha’da shi da hukuma, har yau zuciyata tana mamakin wai ke kika aikata haka?” Iya kufula zuciyata ta kai cika kawai nake ina batsewa na masa banza. Still idonsa a kaina, kafin ya sake burkito ni jikinsa idonsa a runtse yake duk abinda yaga dama da jikina, hannunsa ba inda bai zagaya a jikina ba sai dai idonsa a kulle. A kunne ya ce min “Talk to me, me wancan banzan ya fi ni, da kin bari an kawo ki gida na zan maki soyayya da hot romancing da na tabbatar babu kalarsa a duniya, kin k’arya min zuciyata kin saka min rauni a gabban jikina bani da nutsuwa sam tunda abin nan ya faru, bana iya cin abinci duk k’aunata da abincin, bana iya barcin good 4hours saboda da na rufe ido wancan banzan mutumin nake ga ni, me yasa Aysha ki gaya min yaushe kuka ha’du da shi da kuma me ya rud’eki?.” Ya fa’da yana cusa kansa a k’asan wuya na. Da k’arfin gaske na ture shi ina mayar da numfashi na yi pointing d’insa da yatsa. “Ya isheka Ahmad, kada ka kuskura ka sake kawo kanka jikina, na ji ni karuwa ce ka san da haka me yasa ka dawo da ni gidanka da zaka sani a gaba da surutan banza, sanda abin ya faru me yasa baka same ni mun yi magana ni da kai ba ka kai maganar wajen iyayenmu? Ka tambayeni ka ji na aikata ko ban aikata ba? Ka yi bincike ka ji ni ce ko ba ni bace, meye amfanin tambayar yanzu tunda ka Riga ka yanke a ranka ni ce to amsa guda zan baka Eeh ni ce sai me?” Lumshe idonsa ya yi, yana aikin yamutsa kansa kafin ya furta “Na yi bincike bayan faruwar abin har gidan da aka ce kuna zuwa shai’dananci da daddare na je, na kuma tambayi wasu y’an mata da na nuna musu hotonki suka min shewa suka ce k’warai ke ce har suka sake nuna min wani hoton naki mara kyan gani. Duka wannan ba hujja ba ce?” Na lumshe ido na cikin tafarfasar zuciya na ce “Ni ce Ahmad! And so what?” Murmushi na ga ya yi ya Mik’e ya ce “So nothing, nan gaba kuwa zaki ga something da zai yi hurting zuciyarki.” Ya shige d’akinsa. Ido na bi shi da shi kafin na zauna a wajen zuciyata na tuk’uk’in b’acin rai. Tsawon lokaci na d’auka kafin na mik’e na shige d’akin dana tabbatar nawa ne. Ina shiga na kife a saman gado cikin wani irin matsanancin kuka mai saka tafasar zuciya. Sai da na yi kukan sosai har naji kaina na sarawa, sannan na ji shigowar Ustaz cikin d’akin. Da sauri na lumshe idona kamar mai barci duk da wani zazzab’i ne naji yana ratsa k’asusuwan jikina. Zama ya yi a gefen gadon shirun da na ji ne ya saka ni bu’de idona sai naga nasa idon a lumshe ya jingina da gefen gadon. Muryarsa da yake bayyana damuwa ya ce “Ki tashi ki yi alwala zamu yi sallah.” Na mik’e da sauri na ce “Idan na k’i fa?” Ya zuba min ido yana furta “Dole ma zaki yi, don sunnah ce ga duk ma’aurata kafin su kusanci juna, duk da dai ni ba kusantarki zan yi ba, amma tabbas zan yi romacing jikinki har na samu nutsuwa don na gaji da tara abinda ke jikina, shi yasa ma na dawo da ke.” Ya fa’da yana narkar da idonsa a cikin nawa, kallonsa kawai nake da mamakin furucinsa a zuciye na ce “Sha’awata kake shi yasa ka dawo da ni gidanka kenan?” Ya ‘d’aga min kai. “Lefi ne don na yi sha’awarki? Wasu banza ma suka yi sha’awarki, abinda zai hana ni gurzar ki son raina yau naci alk’awarin kema ba zaki fara sani na d’a namiji ba sai na miki kishiya ba don komai ba sai don kiji abinda na ji ba zaki b’areni a leda ba kamar yarda ban b’areki ba, kuma dole gobe akwai Doctorn da zata zo ta miki test…” wani kalan zabura na yi, ina jifansa da wani kallo. Ya sake d’aga kansa yana murmushi ya d’agan gira. “Oya tashi ki yi alwala Madam, and after the prayer you must remove all your clothes yau zahirin ki nake son gani na more….. Mu ha’du da daddare may be a Arewabooks 😜 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 38… NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Baki na saki kawai ina kallonta ta cigaba da fa’din. “Hmn, ai ni wallahi Ustaz bai kyauta min ba, na zata ke fa zai kawo kusa da mu ya tamfatsa wani Uban gini mai masifar kyau, ga amaryar daga ganinta tana da wayayyan kai kuma ta girme mu sosai a shekaru sai kin dage AYSHA don y’an r gayu ce wallahi, abinda ma ya kawo ni kenan na fa’da miki ki tashi tsaye sosai kada ta k’wace miki Miji….” murmushi kawai nake ina kallonta har ta gaji ta zabga min harara. “Wai ba zaki ce komai ba ne? Ni ya naga kamar ba ki san da kishiyar ba fuskarki looking so exhausted…..” na dafa ta ina jan hannunta muka shiga cikin parlor muka zauna sannan na ce mata “Asma’u ban san Ustaz ya yi aure ba, amma ba zan ce komai ba sai Allah ya bada zaman lafiya ….” Cikin mamaki Asma take kallo na ta ce “Baki sani ba As in how? Ta yaya zai yi aure without you knowing?” Na tab’e baki ina ware hannu alamun ban damu ba sai na ga ta yi turus ta ce “AYSHA you looked not worried? Kan ki d’aya kuwa?” Na ce “Da biyu ne Asma? Baya gabana ne kawai, ya je ya yi ta aurensa bakomai tawa k’addararce haka, ina addu’ar Allah ya bani ikon amsar ta a yarda tazo min.” Jikinta a sanyaye take kallo na. Ta ce “Ba ki damu ba AYSHA?” Na girgiza kai Ina furta “Ban damu ba Asma, me ke gareta? Da zan sawa kai na damuwa? A zatona abinda kake so shi kake kishi… na tsani Ustaz irin tsanar da ba zan ma iya kwatanta miki ba, I hate him wholeheartedly kuma bana jin akwai abinda zai saka nan gaba na so shi, wallahi ko mata d’ari zai aura a yanzu dai ba zai dame ni ba, ba kuma ya gaba na, daga shi har matar tasa ba su isheni kallo ba, ni yanzu kawai ibada na saka a gaba da fatan cikawa da Imani. Rayuwar nan da duk abubuwan nan da suke cikinta wallahi tsoro suke ba ni.” Asma jinjina kai kawai yake kafin ta ce “Wai kina nufin har yanzu baku koma daidai da Ustaz ba?” Na sakar mata murmushi kawai ina mik’ewa na shiga kitchen na samo mata drinks da wasu snacks ragowar na safe da na yi na ci. Bata wani jima ba ta tafi bayan ta gama bani hak’uri sosai ta na sake gaya min AYSHA sai kin dage sosai akan Mijin ki fa…Ina gaya maki waccan matar idonta tar yake kuma billah da shekarunta don idan aka ce zata yi sa’ar sa ma I won’t surprised, so sai kin yi ta kan ki.” Na yi dariya kawai na rakata har gate ta tafi bayan na ha’da mata kayan cosmetics da yawa a leda. Da daddare sai ga Umma Yaya Usman ne ya kawo ta. Kadaran kadahan na nuna mata na yi farin cikin ganinta. Na kawo mata drinks da snacks da bana rabo da su, after na yi warming d’insu a microwave. Ta d’an zagaye idonta da kallo tana furta “Alhamdulillah, dama na san ba zaki bani kunya ba indai ta b’angaren tsaftar jiki da muhalli ce.” Na ‘dan yi murmushi kawai. Ta ce “Sai kika ji labarin Ustaz ya yi aure? To bana son ki saka damuwa a ranki, kishiya dai baa kanki aka fara ba, a gidanku ma mutum biyu kika bu’de ido kika gani, kuma Abbanki ma da kansa ya sake bashi support na k’ara auren, Allah ya bada zaman lafiya ki sake kula sosai banda bin zugar k’awaye, a kuma dinga danne kishi, namiji baya son mace mai zafin kishi da yawa….” Haka dai ta yi ta min nasiha kafin su tafi, ni dai jinta kawai nake ba wai don zan iya kwatanta abinda ta gaya min ko ka’dan na yiwa Ustaz biyayya ba. Ta turo min wasu pack, maza kwashe Kazar sababi ce ta Surayya Dee da garurrukan magani ki sake dagewa da kula da jikinki don shine kima da martabar mace, Allah ya baku zaman lafiya ya kawar da dukkan fitina.” Na amsa da ameen, ina kallo suka tafi bayan Yaya Usman ya jani da tsokana ya kuma yi alk’awarin kawo min matarsa jibi. Ina ta son na gayawa Umma Mami na ta zo sai dai wata zuciyar tawa tana kwab’ata, dole na yi shiru ina kallo Yaya Usman ya ja mota suka tafi. Na dawo cikin gidan ina kallon Kazar da Umma ta kawo min, na d’an tab’e baki ban k’i ci ba na zauna na ci a bata don daga d’and’ana romon na ji ta yi da’di sosai kamar ba kazar magani ba. Na sha tsumin Maman Fareeda sai ga wata gyatsa na yi. Ban yi shirin d’ora abinci ba don na san ba zan ji yunwa ba idan ma naji yunwar zan sha cereals, kawai na kunna t.v ina kallo, zuciyata na ta tunanin me Zan yiwa Ustaz na nuna masa ban damu da aurensa ba. Dabara ce ta fa’do min, don haka na mik’e na isa harabar gidan na kira d’aya daga cikin masu hidimar gidan. Ku’di na bashi da takardar da zai siyo min abubuwan da Zan buk’ata. Ina kallo ya yi d’an turus nima kallonsa nake na ce “Ya ne ko ba zaka je ba?” Ya girgiza kai da sauri ya furta “Idan na dawo zan ajiye a k’ofar kitchen ta baya don Alhaji ya ce koda wasa kada mu sake mu yi wa matarsa magana…” ji na yi kamar na k’unduma zagi, sai dai na dake zuciyata na yi tsaki na ce “Idan ka dawo ka ajiye ‘din, ka danna door bell don na san ka dawo.” Na shige ciki zuciyata a zafafe ina ta mitar “mutum sai shegen kishin tsiya.” Ai kuwa bayan three hours sai ga shi ya danna door bell d’in. Na mik’e na isa k’ofar kitchen d’in ta baya. Duk abinda na rubuta ya siyo min. Na kalli kayan ina murmushi greeting cards ne masu shegen kyau an rubuta Happy married life da wasu frames. Sai da na d’auko biro n zauna akan kujera da niyyar na rubuta sunayensu sai na tuna ban san sunan matar tasa ba. Tsaki na ja na rubuta Happy Married Life You and your new bride…” na warwatsasu ko ina har a bakin k’ofa ta yarda duk tsiyar sa idan ya shigo sai ya gani. Bai zo gidan ba sai bayan kwana biyu, na dinga jin hayaniya sama sama daga bakin gate nan na tabbatar shi ya dawo. Ina kwance saman kujera da y’ar b’ingilar rigata sai black jeans saboda zafin da isheni ko d’ankwali babu a kaina. Korean series nake kallo don yanzu shine abinda suke d’ebe min kewa. Na ji yo azababben k’amshin turarensa hakan ya tabbatar min ya shigo parlorn. Wata tsanarsa naji tana sake bunk’asa a zuciyata hakan yasa na masa kallon gefen ido kawai na gyara kwanciyata. Shiru tsawon lokaci yana tsaye a inda yake da brief case a hannunsa naji ya saki ajiyar zuciya “Ba kya amsa sallama ne?” Tab’e baki na yi na cigaba da kallon da nake ina ji ya tako zuwa inda nake yana furta “Magana fa nake?” Wani kallo na watsa masa kafin na ja k’aramin tsaki na sake mayar da idona kan t.vn. Sai na ga ya yi k’wafa idonsa a kan cards d’in da yake saman center table. Naga ya saka hannu ya d’auka. Wani shegen murmushi naga ya saki ya furta “So ashe kin samu labarin aure na da k’urratu aineey? Shikkenan kin hutar da ni yi miki bayani, na samu kamilar mace AYSHA irin kalar wadda nake so. Na gode da taya ni murnar aure na da kika yi da SWEET HAMEEDA… ya zama wajibi na nuna miki farin ciki na..” kafin na furta komai na ga ya iso inda nake cak ya ‘d’aga ni yana hajijiya da ni cikin parlorn sai da ya wajigani sannan muka zube akan kujera ya rungume ni sosai a jikinsa ya a shinshinar wuya na yana kissing lab’b’ana, tsawon lokaci yana wasu irin abubuwa da jikina kafin ya saki nauyayyiyar ajiyar zuciya ya ce “Thank you AYSHA once again, really really appreciated… farin cikin rayuwata da Sweet Hameeda ne ya saka na manta da ke for a while, tabbas iyayenta ba su yi haihuwar banza ba, na amshi budurcinta a daren farkon mu na aure….” Da matuk’ar zafi na tare shi. “Enough Ahmad! Rashin mutuncinka ya tsaya kaina kawai don include my parents wallahi I won’t tolerate… ina ganin martaba da mutuncin iyaye na…” “oh Really?” Ya fa’da yana min wani kallo a zafafe na ce “Na fa gaya maka ka saurara ehe!” Sai naga ya yi murmushi ya ce “Martabar iyayenki nawa kika zubar AYSHA? Ai ni bakomai tsakanina da iyayenki sai mutunci da girmamawa don na san yaudararsu kika yi, kuma Allah zai saka musu, tunda sun yi iya yin su.” Da wani irin sauri na mik’e na nufi hanyar bedroom d’ina don wallahi zuciyata ta Gaza bana jin zan iya cigaba ina kallon Ustaz.. ina ji ya yi tsaki ya furta “Kyan D’an Miciji….” Ban masa magana ba na shige d’aki, sai sannan na fashe da wani irin kuka mai cin zuciya na dafe k’irjina da na ji yana bugawa da k’arfin gaske… Da daddare bayan na ji sauk’in zuciyata na yi wanka na zura y’ar Riga arm less da skinny jeans na yi zama na a parlor don na san ba dawowa zai yi ba. Abin mamaki sai gashi ya shigo hannunsa rik’e da na wata mace da na tabbatar itace matar tasa, ka’dan ya rage ta kai shi tsawo. Da sauri na mik’e zaune ina zura hijabi na da yake gefe na na saki mayalwaciyar fara’a ina mata sannu da zuwa. Zama ta yi na sake ce mata sannu ba. Ina kallon Ustaz na ce “Amma baka kyauta ba, ai sai kace min AYSHA yau da daddare kina da special guest.” Wani tab’e baki ta nayi min kallon hadarin kaji, naji zuciyata ta yi zafi amma sai na maze. Ina ji ya furta “Honey meet wife AYSHA…” sai naga ta d’an sakar masa murmushin da na tabbatar fake ne, ta ce “Nice to meet you, uwargida.” Na mayar mata nima da fake smile d’in. Ina shirin mik’ewa ya ce “Zauna AYSHA, we have to talk… kina ji na.” Wani kallo masa kafin na ce “With my all ears…” na mayar da kaina akan kallon t.v. “Ba zaki concentrating akaina ba…” ban kalleshi ba na ce “I thought kunnuwa ke ji, so go ahead!” Ina ji ya saki k’wafa. “Jiyo ki kalleni Malama.” Na d’ago kuwa na zuba masa idona cikin wani irin kaifaffan kallo. Sai na ga ya yi saurin saukar da nasa idon, yana taune lips d’insa. Sai da ya muka don kansa sannan ya d’ago. “Wannan mata tace sunanta Hameeda, and I loved her shi yasa na aurota, ina son ki ja girmanki although ta girmeki amma aure ke ya bama girman, and You…” Ya juya yana kallon Hameedan “Ki bata matsayinta na uwargida, tunda shari’a ta bata, bana son k’ananan magana duka ina son ku shi yasa na aure ku.” Na d’ago na masa wani banzan kallo kafin na girgiza kai. “Maganar girki kuma, zan raba shi kwana d’aid’aya after mun dawo daga honeymoon da Hameeda kenan, gobe zamu wuce.” Wata irin dariya na yi wadda tasa har sai da suka kalleni gaba d’aya na ce “Hameeda kike ko wa? Magana d’aya ke gare ni na yafe miki duka kwanakin girki na har yaumul k’arshe a wajena, bana buk’atar girkin kamar yarda bana buk’atar Mijin….” AYSHA ya fa’da a tsawace ban bi ta kansa ba na ce “Kina ji na AYSHA da kike gani ba dawwamammiya ba ce a gidannan wani d’an zama nake na lokaci ka’dan, don haka ki je ku sha amarcinki da Mijin ki Ayshatu ba bak’uwar zafi ba ce…na bar ku lafiya ..” daga haka na shige d’akina ban san ya suka k’are ba. Na dai ji tashin mota hakan yasa na fito ina y’ar wak’ata mai shegen dad’i. Ban san sam yana gidan ba sai da nazo tsakiyar parlor na ganshi kwance a saman 3 seater ya rik’e duka kansa da hannuwansa guda biyu. Tab’e baki na yi na nufi kitchen ruwa ne dama na fito sha, don haka na sha a kitchen d’in na sake fitowa don komawa d’akina na ji ya finciko ni da k’arfin gaske… na fa’da jikinsa. K’ok’arin turesa nake amma ya k’i bani dama. A kunne yake ra’da min “Right now zan yi maganin rashin kunyarki wato kina shirya yarda zaki bar gidan nan ko? To gwara na karb’i hakkina don naga da jikinki kike tak’ama zan maki fata fata yanzun nan idan yaso kya koma karuwancin a matsayin fanko.” Duk turjiyar da nake yi amma ya k’i sauke ni har sai da ya isa d’akinsa ina jikinsa ya saka k’afa ya tura k’ofar d’akin ya murza key ya cire key d’in ban san ina ya kai shi ba don tuni na runtse idona jin yarda ya saka bakinsa ya yage riga guda da take jikina dama net ce rigar hakan yasa duk wasu hallittun jikina suka bayyana. Ya cilla ni saman gadon kafin ya yi light off a d’akin. Duk yarda zan kwatanta abin ba zaku gane ba, duk da zafin da nake ji ban fasa jin Muryar Ustaz a kunne na ba yana kwararato yana furta wayyo AYSHA ya ya na kasa shiga? Kafin na fahimci komai na ji d’if na daina gane komai bayan Muryar Ustaz da na ji ya ce wayyo zan Mutu Eesha ta…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 36. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Wani kalan kallo na jefa masa a time d’in Ji nake kamar na k’unduma masa zagi. Sai dai na dake na maze ina zaune ina faman huci naga ko zai iya saka ni na yi sallahr dole… “Biyayya ga Miji dai dole kamar yarda Abba ya gaya miki idan ba haka ba ki shiga wuta…” Shiru na masa idona na sake tara k’walla. Sai na ga ya nufo wajena da d’an hanzarinsa yana furta “May be kema a matse kike ba zaki iya jira a fara sallahr ba, bari na yi abinda zan yi daga baya a yi sallahr…” ya fa’da yana k’ok’arin ja na tsaye ya ce “Cire kayan zan yi tas, ba wani abu da zaki b’oye min abinda duniya sun Riga sun gama gani.” Ganin inda yake kai hannunsa ban san sanda na doke hannun ba cikin matsanancin b’acin rai na nuna shi da yatsa “Ya isheka Ahmad!” Lumshe idonsa ya yi yana furta “Idan na k’i fa mara kunya, common beb wuce ki je ki yi alwala kafin na murje bakin nan…” Hanyar waje na nufa ina jin zuciyata bugawa zata yi idan na tsaya na cigaba da jin maganganun Ustaz. Da k’arfi na ji ya ja ni jikinsa ya rungume ni tsaf hannyensa a baya na yana furta “Tsaya Malama..” Ban san sanda na gartsa masa cizo ba na fice da sauri na fa’da d’aya d’akin na kusa da wannan naci sa’a da key a jiki na shiga na murza key na kuma bar mukullin a jiki. Bana jin yarda zuciyata take sake tunzira zan iya juriya na tsaya Ustaz ya cigaba da gaya min magana ba tare da na masa illa ba, ba kuma na son ya saka ni a layin marasa tarbiyya. Har bakin k’ofar yazo ya dinga bugu da furta “Please AYSHA bu’de..” har bakin k’ofar na isa murya a zafafe na ce masa “Wallahi ba zan bu’de ba, ai ma gane kuma ba don Allah ka dawo da ni ba saboda jiki na ne jiki na kuma yafi k’arfinka wallahi….” Dariya ya yi sosai kafin ya furta “Jikin da bai fi k’arfin k’azaman maza ba ta yaya ni zai fi k’arfina?” Ban amsa shi ba na cije leb’ena kawai ina jin yarda idona ya soye na daina jin haushin maganarsa kawai tunanin hanyar da Zan bi na rama muguntar sa nake. Ranar dai kam har Asuba ina kan sallaya da rok’on Allah, akan ya bayyana gaskiya. Da safe sai sha biyu na bu’de idona tun bayan sallahr asuba nauyayyen barci ya d’aukeni. Duk da naji zuwan Ustaz da nocking da yake bai saka ni tashi ba sai a wannan lokacin. Wanka na yi na tsantsara kwalliya cikin wani army green brocade d’ina da d’inkin ya yi bala’in fito da duk wata sura ta jikina Pitet ce sosai Kuma yawanci d’inkunan da aka min kenan. Gashi na da yasha gyara na kwantar a saman kafa’duna kafin na kafa d’aurin ture kaga tsiya. Bakina har da jambaki da ya k’arawa bakin kyau. Hakan yana daga cikin target d’ina na son tadawa Ustaz hankali. Sarkin naci! Na fa’da a zuciyata ganin still yana kwance akan kujerar da take babban parlor na idonsa a lumshe parlorn duk ya ba’de da k’amshinsa. Karatun Alk’ur’ani yake saurara. Jikinsa wasu irin k’ananan kaya ne masu masifar kyau ni sai abin ma ya min wani banbarakwai ko don ban saba ganinsa da su ba ne. Juya jikina na dinga yi sosai musamman da naga ya bu’de idon sa a kaina yana lumshe su a hankali kamar mai jin barci. Dangwaliliya sosai nake masa kuma a jikina na ji kallon da yake min har na shige k’ofar da zata kai ni kitchen. Ina shiga na saki dariya na ce D’aya kenan! A kitchen aikina nake na fere Irish ina yi ina bin sautin wak’ar da yake kunnena don ya kashe karatun. Juya jikina nake a lokacin ni kaina mamakin abubuwan da nake yi nake. Saboda ba zaka tab’a cewa waccan AYSHAn mai tsananin kunya ba ce. Jin sa na yi ya jani jikinsa ta baya ya rungume sosai gaba d’aya yabi ya baibaye hancina da mayataccen k’amshinsa “Ba gaisuwa?” Ya ra’da min a kunne cikin wata irin Husky Voice da sauri na runtse ido ina ji ya sake shinshinar wuya na ya ce “Uhmn Aysha? Na ce ba gaisuwa…” Ture shi na fara yi amma ya k’i bani damar hakan. “Ki bari Aysha you are my halal, me yasa kike hana ni? Ki gaishe ni na ce..” “Ba zan gaisheka ba Ahmad.” Madadin ya damu sai naga ya ja karan hancina kafin ya kai bakinsa saman wuyana ya sake shinshina wuyana ya ce “Your perfume makes me….” Sai kawai ya yi shiru yana lumshe ido. Yana k’ok’arin sake ja na jikinsa na yi saurin ture shi ina kallon yanayin da yake bin k’irjina da kallo. “Mugu kawai kada ka sake tab’a ni…” “Ai kuwa kin yi ka’dan dama ace budurwa ce ke dal zan iya d’aga miki k’afa amma ke ai kin zama y’ar hannu wani abin ma sai dai ki koya min….” “AHMAD! ya isheka, na ce maka Is enough ba zan sake tolerating ba, na ji ni karuwa ce Uban wa ya ce ka dawo da ni gidanka, ka cigaba da barina na yi gantalin mana… to ya isheka ba zan sake yafe maka ba ka sake kira na da banzan suna…” Tab’e baki ya yi naga ya fita daga kitchen d’in yana fad’in “Bari na wuce kafin ta kai ki fara duka na, ashe bayan wancan harkar har da rashin kunya kika koyo, koda yake duk wanda zai iya abinda kika yi Ai ba batun kunya a tare da shi…” “Ashe ka sani, ai rashin kunya ma yanzu ka fara gani.” Sai da na gama ha’da break fast sannan na fice da abincin na jere a kan Dinning iya cikina ka’dai na dafa. Gidan ya ba’de da wani irin k’amshi. Na zuba a plate na koma daidai saitinsa na zauna ina cin abincin cike da gwasalo da yanga, ina kuma bin wak’ata cikin muryata mai zak’i. Dubana yake k’asa-k’asa wani irin kallo mai cike da raini da rashin ganin girman wanda akewa shi. Hakan yasa naji tamkar na ha’diye zuciya na mutu duk da ban nuna masa akan fuskata ba. Bak’in cikin ganinsa nake balle na kirashi mijina. Ina kallo ya shiga d’aki ya canja kaya zuwa jallabiya mai shegen kyau ya fito yana zanga k’amshin turare waya a kunnensa yana amsawa k’asa-k’asa kamar baya so. Yana kallona bai fasa wayar ba ya ce “Ki shirya zamu asibiti…dole ne a binciki lafiyar ki don ina cikin ru’dani…” a k’ufule na ‘dago na masa kallon baka isa ba ka yi ka’dan, sannan na ce “Ba zan je ba, ai ba dole aka maka ka zauna da ni ba, idan kaga kana kokwanton lafiyata kawai ka sake ni mana.” Dariya ya yi sosai irin dariyar da ake wa mutumin da ya fa’di magana mara amfani…. “Dole fa ki je asibitin nan idan ba kina son na kira Abba na gaya masa ba.” K’emadagas na masa na mik’e na shige d’akin ina jin a raina ko me za’ayi ba zan je asibitin ba. Tsawon mintuna biyar sai ga shi ya biyoni d’akin waya kawai ya sa min a kunne yana furta “Abba..” ina sallama Abba ya rufe ni da fa’dan da yasa na runtse idona. Ina ji Ustaz ya zira min wani babban Hijab mai kama da julbab brown color kalar jallabiyarsa ya ja hannuna muka fice. Kasa musa masa na yi saboda yarda fa’dan Abba yake nuk’urk’usar zuciyata, har hakan ya bayyana a gabbaina na samu kasalar jiki. Ina ji ya ce “Koda yake ba fa amfanin Hijab d’in tunda dama na yaudara ne duniya ta Riga ta san jikin ki…” runtse idona kawai na yi ina ji ya saka ni a gaban motarsa na furzar da wani huci ina jin Anya zuciyata zata d’auki wannan tozarcin har zuwa ranar bayyanar gaskiya abinda kamar wuya. Duk kalmar b’atancin da na yi niyyar fa’da sai naga ta yiwa wannan mugun azzalimin ka’dan. Muna shiga asibitin muka isa reception sai na ji yana tambayar nurse akwai female Doctor on duty? Mata shigar budurwar ta ‘d’aga kai ta fito da file d’in da inaga tuni ya bu’de don shi ya bata numberr file d’in, muka nufi office d’in Doctor. Kallona matar take tana murmushi ta furta “Congratulations Ahmad for having a beautiful wife…” Naga ya yi murmushi kawai sannan ya sanar mata Test za’a min na H.I.V likitan ta d’an waro ido ka’dan ta ce “But why?” Ya cije leb’ensa kawai idanunsa sun yi jajur ya ce “Nima zaki min, mun manta ba mu yi ba ne.” Sai naga ta saki murmushi ta ce “Alright, hakan yana da kyau.” Ta rubuta mana sannan ta ce Mu je laboratory nasu. Har muka isa Lab d’in zabga masa harara nake cikin jin haushinsa aka d’au jininmu sannan aka ce mu jira a waje. Allah ne kawai yake dannar zuciyata tsawon zaman da muka yi ban rufe Ustaz da duka ba, duk da dai ya ceci kansa da ya ce a yi test d’in har da shi. Ba abinda ya d’aga hankalina don na san bana d’auke da kowace shegiyar cuta. Tsawon lokaci kafin a fito da result d’in. Sannan muka koma wajen likitan. Sai da ta mana nasiha sannan ta bu’de result d’in tana murmushi ta ce “Negative, sam baku d’auke da wannan cutar Allah ya sake kiyayewa.” Mainakon naga farin ciki a fuskarsa sai naga ya saki wani fake smiling haka ya mik’e yana yiwa likitan godiya. Muna shiga mota ya ce “Allah ya ceceki, amma fa ki daina murna dole sai mun sake zuwa wani hospital d’in an sake duba ki, don I don’t trust you anymore.” Na ha’diye wani kalar yawu kafin na ce “And so what? Idan kai baka yarda da ni ba, in dai Allah ya yarda da ni Alhamdulilah!” “Kada ki min rashin kunya, wallahi zan zaneki a banza, baki san yarda zuciyata ke hurting ba ko? Zan huce a kan ki wallahi, ki bar ni na ji ma da abinda ke damuna shashasha” Ya fa’da fuskarsa sam ba alamar wasa.. tsaki na ja na ce “Wallahi ba zan zauna ka dokeni ba, sai dai mu doki juna, shashasha kuwa da ka fa’da sunan mu d’aya…” Waro idonsa ya yi ya ce “Really?” Na ce “Offcourse” ya saki fake smile d’insa ya ce “Bari mu je gida naga ko zaki iya duka na mara kunya, yau kam zan k’ure miki abinda ke saki rashin kunya, zaki san ni ba mate d’in wa’dancan tarkacen samarin naki ba ne….” “Allah ya kai mu.” Na furta ina d’auke kai. K’wafa ya yi kafin ya ja motar a mugun speed ya bar cikin hospital d’in. Daga ranar ban sake ganinsa ba, ko na gansa ma ba ya shiga sabgata sai dai ya harareni ya d’auke kai. Ni ma bana k’asa a gwiwa nake ramawa sai kawai ya tab’e baki ya wuce. Yau ni ka’dai ce a gidan don kwana na biyu ma ban saka Ustaz a gidan ba. Kwance nake akan tattausan carpet d’in da yake tsakiyar parlorn na dinga jin ana nocking a hankali. Bu’de idona na yi a hankali na mik’e na isa bakin k’ofar a hankali na ce “Waye?” Wata murya mai kama da ta Mami na ta amsa da “Ni ce Aysha bu’de…” Da azama na bu’de k’ofar cikin mamaki na ware idona ganin da gaske Mami na ce a tsaye a bakin k’ofar, tana sanye cikin dogon Hijab idanunta a kai na tana sakar min murmushi….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA… 37. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Idona na runtse na sake ware su a kanta, don son na tantance da gaske ita d’in ce. Bata bari na cigaba da tunanin da nake ba ta kama hannuna tana sakin murmushi ta ce “Ayshatu ni ce dai ba wata ba, mu je ciki ko ba kya maraba da gani na, na ga baki welcoming d’ina ba.” Jiki na a sanyaye na bi bayanta ganin yarda ta shige cikin parlorn kai tsaye ba tare da wata fargaba ba. Allah ne kawai yasa na koma cikin parlorn saboda yarda k’afafuna suke kakkarwa. Me Mami tazo yi? Shine abinda nake ta tambayar kai na. Zama na yi a kujera mai kallon tata jikina a kasalance ina kallonta kawai. “Ba gaisuwa AYSHA?” Na ha’diye wani yawu da naji ya tsaya min a mak’ogaro na ce “Akwai Mami, ina yini?” Ta sake murmushi tana zagaye parlorn da idanunta. Ta furta “Lafiya lau Ayshatu, ya amarci hope komai ya wuce Ustaz ya karb’eki as his wife?” D’aga mata kai na yi. Sai naga ta tab’e baki ta ce “Allah ya baku zaman lafiya, amma ban gane ba haka ya kamata ki welcoming bak’i ko kuma nice ba ki so zuwa na ba?” Da sauri na girgiza kai ba wai har zuciyata naso zuwan nata ba sai don ba yarda zan yi da kunya na kalli idonta na ce ban so zuwanta ba. Ta saki dariya ka’dan tana furta “Na san you are not Happy Shatu, baki farin cikin gani na ba, ba yarda za ki yi ni, an gina wata Katanga ta k’iyayya tsakaninmu akan laifin…” Ta ciji bakinta wasu tarin k’walla na zubo mata ta furta “Bakomai shai’dan ne, kema kuma ina son ki saka a ranki ba laifin kowa ba ne sai na shai’dan shi duk ya assasa duk wannan wutar fitinar, ki yi biyayya ga Ustaz AYSHA amma ba irin biyayyar da zaki cuci kan ki ba, ki kima jajirce ki koma makaranta bana son nan gaba ki zama a sahun gidahumai nafi son a ko ina a dinga damawa da ke.” Ta mik’e tana murmushin da kai zan iya kiransa feck smile, ta ce “Am leaving Shatu, dama na so kawai nazo na ganki ne…” Ko kafin na ce komai ta nufi hanyar waje da sauri na bita da ledar da ta Bari a saman center table na ce “Mami you forgot your things…” Ta dubi ledar hannu na ta ce “It’s yours AYSHA, duk yarda zaki amfani da su na rubuta.” Ta shafa kumatu na bayan ta kai min sumbata a gefen kumatu ta ja karan hancina ta ce “Take care care of your self dear.” Ta fice da sauri ta nufi gate. Hawaye na ji sun fara zuba a idona na ja jikina da ya min bala’in weak na shige cikin parlor na. Haka kawai na samu kaina da zama jigum cikin rashin kuzari ina kallon ajiyar ledar Mami, na saka hannu na bu’de ta. Wasu irin turaruka ne masu bala’in k’amshi kana ganin kwalabansu ka san an kashe ku’di wajen siyensu. Sai wani body mist da Turarukan wuta na jiki da na kaya. Gefe guda kuma wasu containers ne da aka zubo magunguna iri iri, da tarkacen su zuma, dukkansu da yarda za’a yi amfani da su. Na lumshe ido na ina jin yarda suka sake cika da hawaye. Na tattara kayan na shigar da su bedroom d’ina, haka kawai yinin ranar sai na ji zuciyata ta yi wani irin nauyi ga kasala da ta addabi jikina. Da yamma ina kwance a parlorn idona a lumshe barci ne yake fisgata sai dai bana son na yi barcin duk da daddare ba barcin nake ba, kwana nake ina sallah sai Asuba yawanci nake barci. Na dinga jin k’amshin Ustaz a hancina, a hankali na bu’de lumsassun idanuna sai kawai naga Ustaz a kujerar da take facing d’ina ya zuban ido. Ban ma san ya shigo gidan ba. Fuskarsa a d’an ha’de yana murza goshinsa ya ce “Baki iya gaisuwa ba ne?” Shiru na masa kafin na turo baki na na sake lumshe ido na a raina ina cewa sai ka shekara a wajen in dai jira kake na gaisheka. Tsaki ya yi ka’dan ina kallo ya tashi ya shiga d’akinsa sai naga kamar duk jikinsa a gajiye yake, don a hankali yake tafiya hannunsa a kansa yana jan gashin kansa. Na ja k’aramin tsaki ina sakin wak’ar da na tabbatar ya san habaici nake masa. Bai kula ni ba ya shige hanyar da zata kai shi bene inda zai hau sama. 1 hour ya d’auka sai ga shi ya sauka sanye cikin wando three quarter da armless Riga black da ta yi matching da light cbrownn d’in wandon, da dai shiri muke da shi da kam na furta masa ya yi kyau duk da fuskarsa a tsare take. Ya zauna still yana sake kallo na duk parlorn ya sake ha’dewa da shegen k’amshinsa mai kassara nutsuwar mutum. Tsawon lokaci idonsa a kaina kafin na gaji na ce “Ni fa kallon nan ya isheni malam, wai me ma kake kallo ne?” Lumshe idonsa ya yi kafin ya furta “Mara kunya kawai, me Zan kalla banda abubuwan da ake kallo a jikin mace, wanda kike rabawa maza.” Shiru na masa ba tare da na bayyana damuwata ba sai can na ce “Na raba musu d’in kuma wallahi baka ji yarda suke zuzuta lamarin ba…” wani irin Zillo naga ya yi ya iso gaba na fuskarsa a mugun ha’de ya ce “Are you mad kike gaya min wannan maganar? Ni kike gayawa wasu banza sun zuzuta ni’imarki?” Dariya na yi ina kallon yarda yake wani irin huci kamar zai ci babu. Na ce “Ai gaskiya na gaya maka, don kam duk wanda ya kusance ni sai ya yi kamar ya hauka ce don d’imaucewa…” wani irin fisga ya kai min a zuciye na fa’da jikinsa ya saka hannu zai tsinka min mari sai naga kawai ya saki tsaki ya ture ni gefe idonsa a runtse ya furta “Stop it AYSHA I hate this nonsense, kin san yarda kike hurting zuciyata kuwa? Ko kina son ki yi ma amaryata asarata ne?” Na tab’e baki na ina kallon yarda idonsa suka wani firgice mai nuna yana cikin matsanancin zafin zuciya. Ya mik’e a zafafe ya shige d’aki. Haka kawai na ji ina son na bisa d’akin naga me zai yi. A hankali na tura k’ofar bedroom d’in da ya shiga ina lek’a wa alamar shashshek’ar kuka na ji, jikina a sanyaye na koma parlorn ina mamakin kukan me zai yi, ba shi ya jawo na gaya masa magana ba, ai kuwa zai sani tunda na gane ba zai iya jure kalamai na ba, ko da su ka’dai sai na dinga hurting masa zuciya, har ya gaji ya daina jifa na da kalaman b’atan ci. Har Magriba ina parlorn ban mik’e ba, shima still bai fito daga cikin bedroom d’in ba. Sai da aka kusan kiran sallah naga ya fito da alama wanka ya yi jikinsa sanye da jallabiya fara tas gashinsa a kwance sai k’yalli yake. K’afarsa sanye da wani black silifas da ya fito da kyan k’afar tasa. Kallo guda ya min ya ‘d’auke fuskarsa a d’aure ya ce “Ki dafa min Indomie, ki shirya kuma zamu gidanmu anjima.” Bai jira amsa ta ba ya wuce. Harara na wurga masa ina tab’e baki na ce “Wallahi ba zan dafa ba. Gidanku kuma zan je ba don komai ba sai don kada ka ha’da ni da Abba mugu kawai mai kan tumato.” Bai dawo gidan ba sai da aka yi sallahr Isha’i. Ya shigo da manyan litattafai a hannunsa. Sama ya shige sai ga shi ya sauko. Ya ce “Ina indomien?” Na d’auke kai ina fa’din “Ban dafa ba…” ya girgiza kai yana fa’din kin yiwa kan ki, gobe i yanzu ma ba zaki ganni ba balle ki wulak’anta ni. Tashi mu tafi, ko shima ba zaki ba?” Ban masa magana ba na mik’e ina roller mayafin abayata ya d’an kalleni sama da k’asa ina ji ganin da ya yi abayar bundumemiya ce kamar Boubou sai bai damu ba ya nuna min hanya. Shi ya kulle k’ofar babban parlorn sannan muka fita. Tunda muka fita karatun kur’ani kawai ya saka cikin suratur rahman har muka je bai ce min komai ba, nima ban ce masa ba. Sai da ya yi parking a babban parking space d’in gidansu na saka hannu zan bu’de k’ofar na jita a kulle. Juyowa na yi ina kallonsa idonsa ma a lumshe yake na ji yana furta “Idan kin shiga kuma, ki yi behaving like mara kunya kamar yarda kike min a gida, ba ruwana ke zaki zama mai bak’in jini a wajen dangin Miji da Uwarsa…” Turo baki na yi na furta “To ina ruwana sai me?” Waro ido ya yi kafin na ji ya jawo ni da sauri jikinsa duk da k’ok’arin k’wace wa da nake sai dai ya ha’da bakina da nasa ya min wani irin tsotsa a gaggauce yake murzar leb’ena da nasa bakin yana romancing jikina cikin wani irin gigitaccen yanayi. Ban wani hanasa ba don da haka nake son cin galaba a kansa. Sai da ya yi son ransa sannan naga ya sake ni ya kifa kansa a saman sitiyari, yana mayar da numfashi ya furta “Gobe ma ki sake saka jambaki idan zaki fita kin ji?” Ya fa’da cikin wata irin murya. Shiru na masa ina kallon yana danna wayarsa ya saka a kunne bayan an d’aga wayar. “Fito maza ki shiga da ita Habibteey akwai inda zani.” Ya kashe wayar yana min duban k’asan ido, ya furta “Kin jawo ba zan iya shiga cikin mutane a haka ba, dole za’a gane ni, wai ke dole sai kin ja ra’ayi na shine har da saka jambaki da turare ko?” Ya fa’da yana sake kai kansa k’irjina ya shinshina da kyau ya furta “Duk mace mai saka turare dai idan zata fita Manzon Allah ya tsine mata.” Na ture kansa a jikina ya d’ago yana kallona cikin tsare gira ya ce “Don’t tried it again, duk sanda kika sake ture ni daga halak d’ina you will see what I do, mara kunya gantalallen jikin naki ma..•” Isowar Khadija ne yasa ban mayar masa da martanin maganarsa ba, na yi sak ina kallonsa hakan ya saka ya hura min iska a fuska bayan haka ya manna min kiss a gefen kumatu a hankali ya furta “Be a good girl, don’t behave like….” Sai naga ya yi tsaki ya bu’de k’ofar na ce “Ka k’arasa mana.” Hannu na da Khadija taja cikin farin ciki ne ya hana ni k’arasa maganar, ta rungume ni tana furta “Oyoyo Anty Ayshan mu.” Na d’an yi murmushi kawai ina kallo Ustaz ya fito daga motarsa ya nufi ainahin chalet inda d’akunansu suke. Khadija ta ja hannuna muka shiga cikin gidan, tana ta min surutu da nuna min jin da’dinta da gani na da ta yi. Ta ce “Ina ta son zuwa Anty AYSHA, Bro ne ya hana ni zuwa wai bai gama cin amarci ba zan zo na dameku da surutu.” Murmushi kawai na saki ina mamakin shegiyar k’aryar Ustaz. A yarda Mahaifiyar su ta karb’eni na san sam bata yi farin ciki da zama na surikarta ba, ta dai amsa gaisuwata ta ce a kawo min drinks Daga haka bata da’da bata raga ba, lamarin da ya sanyayar min da zuciya na dinga jin kamar na saka kuka, na tuna wancan lokacin da nazo da ta dinga yin kamar ta mayar da ni cikinta. Ban wani jima ba Ustaz ya yiwa Khadija waya ya ce ta fito da ni zamu tafi. Ina kallon wani banzan kallo da Mommy ta min da ina mata sallama ta ce “Allah ya bamu alheri.” Na fice jikina a sanyaye na bi bayan Khadija da itama na lura sam bata ji da’din abinda Mommyn ta yi ba. Don a hanya ta ce min “Sai hak’uri AYSHA, kin san lamari irin wannan…” na d’aga mata kai ina sakin fake smile. Tunda ya mayar da ni gida ban sake ganinsa ba tsawon kwanaki shidda, sai dai hankali na bai wani tashi ba musamman da na tsinci wata takarda a saman dinning da ku’di a kai ya rubuta “Ko zaki buk’aci wani abu, kada ki neme ni na yi nisan kiwo.” Na ja tsaki na yaga takardar ku’din kuwa ko kallonsu ban yi ba. Ranar da ya kwana shidda da tafiya ina kwance wajen 11:30 na dinga jin nocking a babbar k’ofar shiga parlorna. Na mik’e jikina sanye cikin atamfa ban damu da tambayar waye ba don na san ba zai wuce Ustazu ba. Na saka hannu na mur’da handle d’in sai idona ya fa’da cikin na Asma k’awata. Da murmushi ta ce “Amare, kun yi wuyar gani, koda yake yanzu Uwargida sarautar mata zan ce.” Sam ban gane furucinta don haka na tab’e baki na ce “Asma yanzu idonki kenan?” Ta ha’de rai tana furta “Kya ce haka mana, yaushe rabon da ki neme ni ko a waya.” Na tab’e baki na ce “Ina naga wata waya, ni Ai yanzu ba ni da waya haka nake rayuwa kamar wata y’ar prison, ya su Mama?” Ta ce “Haba dai, har yanzu wai kina nufin baki da waya?” Na d’aga mata kai ina d’an murmushi sai naga ta saki ajiyar zuciya ta ce “AYSHA ya kika ji da fargabar kishiya kuma? Ni fa wallahi na zata ke Ustaz ya kai gidan da yake gina wa na kusa da gidanku, ina ta murna zaki sake zama mak’otanmu, wai sai jiya na shiga in k’are miki tsiya kawai naga Ustaz da wata banza a zaune a parlor ta bi ta kanainaye shi, na dinga zare ido ina kallonsu sai na ji ta ce “Zauji wacece wannan? Na ji Ustaz ya ce aminiyar Uwargida ce. Wallahi ban san sanda na fita daga gidan ba a gigice….” “KISHIYA?” Na furta ina kallon Asma? Sai na ga ta yi tsilli tsilli ta ce “Ba dai baki sani ba?” 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA… 40. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. (WhatsApp only pls!) Ji na yi k’irjina ya buga da k’arfin gaske, da sauri na saka hannu don na amshi wayar sai dai Mommy bata bani damar hakan ba, ta rik’e wayar gam a hannunta, tana jifana da wani irin kallo da ban isa na musanya mata abinda ta gani, amma cikin k’arfin hali kuma once a rayuwata na tab’a yin k’arya da wayo na dai. Na ce ba ita ba ce Mommy, sharri ake son k’ulla mata…” Ta dubi numberr da aka turo sak’on sannan ta mayar da kallonta kai na ta ce “Shi Shareef d’in ne zai mata sharrin?” Na yi saurin girgiza mata kai, zuciyata na wani irin bugu ga damuwata ta kasa b’uya a idona, na yi nadamar ajiye hoton a wayata d a vedion ma gaba d’aya, na san tabbas sai Mommy ta nemi Shareef don jin gaskiyar lamari. K’wafa naji ta yi ta kuma cilla min wayar tana furta “Mazinaciya kenan zaka aura Ahmad? Ka sani amma so ya rufe maka ido, zaka iya rantse min da Allah wannan ba AYSHA ba ce? Ga kamanninta nan zahiri amma kana son ka raina min hankali, amma wallahi ka bari na tambayi Shareef ya tabbatar min ita ce wallahi ko itace autar maza ba zaka aureta ba, ka ji na gaya maka?” Na ‘d’aga mata kai duk da rawar da zuciyata take yi. Tana fita daga bedroom d’in na yi saurin kiran Shareef a wayata. Tun kafin ya yi magana na ce “Please Shareef do me a favour please..” Shareef da yake ji na ya ce “Wai menene Ahmad, ka gaya min mana.” Na ha’diye yawu da k’yar na ce “Ko Mommy ta kiraka ta tambayeka AYSHA ce a vedion nan ka ce ba ita ba ce ka rufa min asiri, wallahi ba zan iya rayuwa ba Ay….” tsaf furucin baki na ya ‘d’auke ganin Mommy a tsaye a kaina da alama ta ji duk abinda nake fa’da daga kallon da take min mai kama da zata kai min duka. Wata dariya ta yi ta girgiza kanta. “Wato Ahmad ka amince ka saka kanka a bala’i ko? Ka yarda zaka auri Aysha ko da karuwa ce ko? To wallahi sai dai idan ni Uwarka ba na raye, ba shashashar uwa ba ce ni da zan bari a gurb’ata min zuri’a da b’aragurbi, Allah na gode maka da bata kai ga tarewa ba, a yanzu nake son ka saketa wallahi ko na yi maka baki shashasha kawai…” wata irin zufa ce ta dinga zubo min, ban san sanda na isa gabanta ba na zube gaba d’aya cikin rawar murya na ce “Please Mommy don Allah ki rufa min asiri wallahi son AYSHA ne zai kashe ni…” wani kallo ta min ta ce “Sai dai ka mutu kuwa? Don wallahi ba zan fita daga d’akin nan ba sai ka saketa kuma idan ka k’i bin Umarni na zan rok’i Ubangiji ya mana sakayya tsakani na da kai…” Kaina na ji ya wani irin sarawa na runtse ido da k’arfin gaske na ce “Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna ina kallon farar takardar da take mik’o min. “RUBUTA Ahmad tun kafin taron jama’ar nan su san me ya faru…” Na dasa biro akan paperr sai dai rawar da hannuna yake yasa na kasa rubutun sai da Mommy ta sake daka min tsawa sannan na rubuta saki guda. Na ninke ina runtse idanu zuciyata na min wani irin suya. Ina kallo Mommy ta fita daga d’akin cikin dishi dishin ido na da hawaye da suke zuba. Na kifa kai na akan gadon ina kuka, a daidai lokacin kuma kika dinga kira na akan na zo na kai ki wajen dinner shine dalilin masifar da kika ji na miki a cikin waya ta gefe guda ke nake jin haushi ina tunanin komai ma ya samu da auren mu ke kika janyo. Mutane suna watsewa Mommy ta shigo bedroom d’ina, tana furta “Ka tashi Ahmad yanzun nan ka kai mata takardar nan, kuma wallahi idan baka kai mata ba a daren nan ban yafe maka shayar da kai da na yi ba, haka nan bana buk’atar ka gayawa kowa umarnin da na baka har sai ka kai mata sakin nan, don ko sama da k’asa zata ha’de ba zaka zauna da yarinyar nan ba…” Na share zufar da ta keto min ganin ko ta ina ba ni da wata mafita Mommy ta min dabaibayi. Sanda na iso gidan na tabbatar an kawoki zuciyata tana harbawa na isa d’akina. Hannuna rik’e da takardar da na kira da Black paper. Ban shiga gidan ba sai da na siya miki komai saboda ba zan iya baki takardar hannu da hannu ba shi yasa na saka miki a cikin kaya, wallahi A lokacin da kika shigo d’akina kina kuka dauriya kawai nake ban kai ga zubewa ba, duk wata gab’a a jikina rawa take ina tausayin kai na ina tausaya miki. Ina jin sanda kika fita daga gidan zuciya ta ta dinga bugu ina fatan Ubangiji ya zare min damuwa, banda ni musulmi ne da na rok’i mutuwata a wannan ranar. Na so na b’oyewa y’an uwanki abinda ya faru amma shima Mommy ta ce ban isa ba…… Bugun k’ofar da ake ne yasa Ustaz ya zare jikinsa daga nasa, ya manna min kiss a lips d’ina sannan ya fita. Bin bayansa na yi da kallo ba wai don na yarda da abinda ya ce ba, sai dai wata zuciyar tawa tana son ta tabbatar min da Ustaz gaskiya yake fa’da. Na d’an cije leb’ena bana jin zan yafewa Ustaz da kowa ma, jira nake kawai gaskiya ta bayyana na nuna musu tsagwaron fushi na, ba zan zauna da shi ba tunda Mommynsa bata so na bata kuma yi min uziri ba. Abinda ya fi ban haushi kishiyar da ya min, ina kuma makomar dank’ara min magana da yake, duk da bai kai k’arshen labarinsa ba zan jira na ji k’arshen, amma bana jin zan masa afuwa. Ciwo jiki na yake sosai ga k’asa na da yake wani irin ra’da’di kamar borkono. Umma ce da wata mata da na tabbatar Y’ar Uwar Mommyn Ustaz ce suka shigo bedroom d’in. Ustaz kam bai biyo bayansu ba ba mamaki kunyar abinda ya aikata ya ke. Ina ganin Umma na sake sakin kuka ina cije baki da y’ar shagwab’a na ce “Umma wallahi zafi na shiga uku Umma na…” Kallo na ta yi cike da tausaywa na san ko ban yi bayani ba sun san me ya faru daga kallon da naga sun min. Doctorn ta ce “Sannu banda raki Daga haka girma yake kama kowace mace. Bari na duba ki Naga idan zan iya treatment anan na maki, idan kuma sai an je Hospital dole mu tafi.” Na runtse ido na jin ta ce wai na bu’de k’afata. Kunya ce ta kama ni bana son bu’de war sai da Umma ta ce “Gyara mana AYSHA, ai dole sai kin gyara sannan zata san abinda zata miki.” Na d’an kauda kai na sannan naga likitan ta saka hannu ta d’an bud’e cinyoyina da sauri na ji ta ce “Hasbunallah me ya shiga kan Ahmad haka ya ji miki wannan raunin? Ai ba a shiga jikin budurwa da k’arfin gaske haka, yanzu gashi nan ya miki rauni sosai….” ina kallo Umma ta d’an d’auke kai sai dai ta saki murmushi ka’dan Fuskarta kuma ta bayyana walwalar da zuciyarta take ciki, da alama ita bata damu da raunin da Ahmad ya min ba kenan. Ina ji ta kalli Doctorn ta ce “Kina nufin AYSHA ta kawo budurcinta?” Likitan ta d’an kalleta zata yi magana suka ji an turo k’ofa muka mayar da kallon mu akan k’ofar Mommyn Ustaz ce ta shigo fuskarta a ha’de… (Kun San bani da lafiya ku yi hak’uri da wannan. Na gode da addu’oinku masu kiran waya masu text duka na gani na kuma yaba Jallah ya fi ni yabawa. Allah ya bada lada.) 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 39…. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Da k’yar na bu’de idona, ina jin yarda kamar aka rirrik’eni tsam ba ta yarda zan juya. Sai yanzu memory d’in abubuwan da suka wakana suka dawo min. Wani irin zafi jikina ya ‘d’auka, da alama zazzab’i ne ya kama ni. Na yi k’ok’arin juyawa sai dai n kasa, cikin wata irin murya na ji ya ce “Sleep Eehsha.” A zafafe na yunk’ura da niyyar tashi cikin wani irin zafi da tafasar zuciya. A hankali Na ja Ustaz ya sake rungumeni sosai a jikinsa, ni sai na ji ma kamar nasa jikin shima zafin ya ‘dauka. Kiss ya kai min a gefen kunnena sannan ya ra’da min “Sleep mana, bana son ki tashi…” na samu da k’yar na turesa daga jikina cikin k’arfin hali duk da azabar da nake ji sosai a jikina. Amma na gwammaci azabar da na cigaba da zama a jikin Ustaz da nake gani tamkar bak’in kumurci. Na samu da k’yar na matsa daga jikinsa ina jan bargo don suturce jikina. Gani na yi ya sake matsowa a zafafe na ce “Kada ka sake matsowa jikina Ahmad! I hate you…” muryata ta sark’e sabida kukan da yazo min ga wata irin azaba ina ji a k’asana. Bai fasa matsowar ba kamar yarda nima ban fasa masa masifa ba ina ja da baya, har ya cimma ni a k’arshen gadon, hakan yasa na wawuri side bed lamp da take gefen gadon na Rotsa masa a kai. Ina kallo ya dafe wajen sai kuma ya bu’de lumsassun idanunsa yana kallo na. Na ce “Ka zata da wasa nake da na ce kada ka matso ni, wallahi ka sake zuwa inda nake sai na maka abinda ya fi wannan na tsaneka na gaya maka….” Shiru ya yi yana shafa jinin da yake zuba daga gefen fuskarsa mai yawan gaske. Ina kallo ya sauka ya shiga toilet ban san me ya yi ba ya dai d’au tsawon lokaci a ciki ni dai ina kwance banda kuka ba abinda nake, ga jikina duk kakkarwa yake saboda azaba da ta isheni. Idona a lumshe na ji ya fito daga toilet d’in, na d’an bu’de lumsassun idanuna sai na gan shi daga shi sai towel da ya d’aura a jikinsa gaba d’aya jikinsa a bu’de yake, ya k’araso inda nake, wajen da naji masa ciwo ya fito sosai don glass d’in fitilar ya shige shi, wajen ana hango nama ya yi fari tas da shi. Ya min d’aukar cak gaba d’aya irin d’aukan da ake ma Babies. Bani da k’arfin da zan iya mutsu mutsu don haka na yi luf a jikinsa ina ji ya saka ni cikin ruwan ina k’ok’arin tashi ya rik’e ni gam a jikinsa kafin shima ya shiga cikin ruwan ya rik’e ni sosai ta yarda ba zan iya ko motsi ba. Busa min kunne kawai yake yana fa’din “Relax my Baby, I know it’s hurting you ko? Ki rabu da Ahmad zan yi maganin sa ki yi shiru…” Shirun kuwa na yi bayan na turo baki na ina sake kukan da ban san dalilinsa ba. Tsawon lokaci yana gasa ni kafin ya sake d’aukoni still kamar jaririya ya fito da ni. Riga ya zura min ya bani hijab “Ki yi sallah kin ji Baby na, I will come back soon zan je na samo Doctorn da zai duba ki ya min dressing wajen nan.” Na zumb’uro masa baki ina sakin kuka saboda wani irin zafi da nake ji still a k’asa na. Ustaz ya ja ni jikinsa ya rungume “Ki yi shiru mana, ko ba kya son na fita.” Ban fasa kukan ba kuma ban amsa masa ba. Naga ya danne wajen da yaji ciwon da tissue hannu guda ya kuma yana bubbuga baya na. “Ki yi Sallah, zaki makara past 7:00 fa…” Ko zama ba zan iya yi ba balle na yi sallah saboda yarda nake jin wurin hakan yasa na ce masa “To a yaya zan yi sallahr bayan wajen zafi yake min?” Shiru ya yi a idonsa nake kallon tausayin da yake min ya ce “Zaki iya yi a kwance Ai, tunda lalura ce, pls forgive me AYSHA wallahi ban san sanda na aikata ba hankalina ne at all ya bar jikina.” Na juya kai ina furta “Ko mugunta ba..” Murmushi ya saki yana gyara min kwanciyata sosai ta yarda nake kallon gabas. Na tada sallahr ya fita bayan few minutes sai gashi ya dawo da Hot coffee mai zafin gaske. Tsayawa ya yi a kaina yana furta “Kin idar AYSHA?” Ban amsa masa ba illa ido da na zuba masa. Ya kamani ya d’aga ya wara cinyarsa ya d’orani a kai ta yarda zan zama ba zan kama ciwo na ba. Sai da ya bani peck a lips d’ina sannan ya ‘dora cup d’in a bakina. A hankali na dinga sipping ina raki. Na sha rabi kafin ya mayar da cup d’in ya ajiye ya b’alli pain reliever ya saka min a baki. Ina runtse ido na sha saboda baya min da’di. B’ata fuskar da nake yi ne ya saka shi bu’de baki na ya saka harshensa yana tsotse nawa harshen yana saki ya yi dariya yana fa’din “Kin daina jin d’acin?” Turesa na yi na koma kan gadon…. Ina sake sakin kuka saboda fama wajen da na yi. Ina kallo yana ta ignoring kiran da ake masa, har daga baya na ji yaji wani sabon ring tone da sauri naga ya ware ido ya d’aga kiran yana cigaba da massaging jikina na ji ya ce “Mommy is not like that…. Kawai dai ina ganin tafiyar ba zai yiwu ba ne, Saboda AYSHA is seriously sick….” Gani na yi ya b’ata fuska ya ce “To tafi ita ka’dai mana Mommy, ta ya zan tafi na bar y’ar mutane ba lafiya alhali ni na mata causing ciwon…” Ya kashe wayar sai naga idanunsa sun yi ja ya d’an rik’e kansa kawai yana tsaki bayan wani kiran ya sake shigowa wayarsa… ya d’aga a fusace ya ce “Look Hameeda ba inda za ni yanzu, idan da ni na ce zan je yanzu kam ba zani ba and so what? Shine har da zuwa ki gayawa Mommy you think hakan Daidai ne, na yi disvirgining yarinyar sannan na tsallake na barta?” Daga haka ya kashe wayar yana zanga tsaki… wayarsa ya sake kira ina ji yana fa’din “Please Anty don Allah kizo ki dubata, ina gida.” Ya ‘dan yi shiru sai kuma ya ce “Alright thanks sai kin zo.” Ya ajiye wayar yana d’an sunkuyowa ya yi kiss kunnena ya ce “Yanzu k’anwar Mommy zata zo ta duba ki, am sorry ko?” Shiru na masa zuciyata na wani irin tafasa sai dai ba zan hana ta ta zo ta duba ni ba, ko bakomai zata je ta gayawa Yayarta na kawo budurcina. Muryata a raunane na ce “Ni gaskiya ka kira min Umma.” Ya waro ido yana furta “Umma kuma Aysha? Ta ya zan kalli Umma da wannan aika aikar da na yi Ai kamar da kunya ko?” Na tura masa gida ina alamar zan yi kuka ya yi saurin ja na jikinsa ya ce “Okay, It’s Okay kada ki yi kuka zan kira ta but ke zaki mata magana.” Na d’aga masa kai sai naga ya kira ya saka min a kunne. Talk…” Ya ce yana marairaice min alamar kada na fa’di gaskiya, na tab’e baki a raina na furta “Mhmn ai wallahi sai na fa’da, bayan abinda nake so su sani kenan… Umma tana d’agawa na ce “Umma ba ni lafiya zan mutu… please ki zo zan mutu…” Ustaz ya kashe wayar gaba d’aya ya yi switching Off. ya jani jikinsa yana sakin ajiyar zuciya a hankali ya ce “Pls AYSHA ki yafe min, duk da Wallahi ban tab’a yarda da cewa zaki aikata zina ba dama….” “yanzu ba…” na furta ina ture shi jikina ya sake jana jikinsa ya ce “Wallahi am serious Eehsha, na dai shiga tashin hankali ba d’an ka’dan ba… wallahi wallahi AYSHA na san ba kya zina, na san kuma baki aikata ba. Ba yarda zan yi ne a lokacin an saka ni a cikin wani irin dabaibayi. Sanda abokina yazo ya same ni da maganar ya kuma tura min hotunan na ji zuciyata ta wani irin harbawa. Ina murmushi na ce masa sam ban yarda ba, ba AYSHA ba ce wannan, idan kuma kana son na yarda kuma sai ka kai ni wajen mutumin da ya baka hoton ko kuma shi saurayin da ka ce suna mu’amala? Ya amsa da sauri alamar zai yi duk abinda na ce. Sanda muka yi waya da shi ya tabbatar min a lokacin ma kuna tare, cikin mamaki na ce ko zai iya turo min vedion da zai nuna kuna tare. Bai wani jima ba ya turo min vedion, a wannan lokacin suma ne kawai ban yi ba, jikina ya dinga kakkarwa musamman da na kira ki a waya ta dinga ringing baki d’aga ba, k’arshe aka ce min an kashe wayar. A lokacin tabbas shai’dan yaso ya rinjaye ni sai dai na dinga yak’i don hakan ba don komai ba sai don zuciyata ta kasa yarda da cewa ke ‘din ce. Na koma gida cikin matuk’ar karayar jiki da na zuciya. Tabbas a rayuwata ban tab’a shiga tashin hankali kamar na wannan lokacin ba. Ina zuwa gida na shiga bedroom d’ina na kulle ina sakin kuka zuciyata na gaya min ba ke ba ce amma wata zuciyar na gaya min ke ce. Duk da sanyin Acn dake d’akin bai hana gumi tsatstsafo min ba. Yini guda ranar na k’i shiga cikin gidan mu, har Mommy ta gaji ta aiko kira na sai dai na musu k’aryar bakomai. Tunani na kawai ta yarda zan gano bakin zaren. Da la’asar bayan na dawo daga sallahr la’asar na kira abokina shareef na dinga rok’onsa akan ya gaya min gaskiya shin abinda abokinsa ya fa’da gaskiya ne ko biyan sa aka yi? Shareef murmushi ya yi ya kira mutumin a waya take ya tabbatar min kun kai tsawon wata shidda tare da shi…” k’it na kashe wayar duk wata kafa ta jikina zubar da gumi take, naji duk duniya na tsani mata amma madadin soyayyarki ta ragu a zuciyata wallahi sake k’aruwa ta yi, hakan yasa nasan lallai son ki it’s part of my destiny. Zuciyata ta kulle gaba d’aya na rasa mafita, zazzafan zazzab’i ya rufe ni a gidan su Shareef. A yammacin ranar kuma duka bak’i suka cika gidanmu. Ban ji zan iya fasa aurenki ba Aysha a lokacin, don zuciyata gaba d’aya ta Riga ta mamaye da k’aunar ki sai dai na saka a raina dama kafin na tara da ke zan saka a bincika min ke a asibiti, hakan na yanke a zuciyata na ji kuma koda ya kasance ke mazinaciyace zan hak’ura na aureki na kuma rufa miki asiri. Ba zan gayawa kowa ba. A haka aka shiga biki sosai, kowa ya ganni sai an min kirarin ango, ni dai kawai murmushi nake na dinga jin zuciyata na wani irin duka a duk sanda na tuna wancan hoton. Sai dai na bar shi as evidence a cikin wayata ban goge ba. Da yamma muka sake zuwa gidan da ka ce min kuna zuwa a lokuta da dama ke da wancan saurayin. Sanda muka je muka nuna hotonki sai wasu y’an mata Suka tabbatar min sun sanki sunanki Aysha ina jin sun fa’di haka na runtse ido na kawai don bana son maganar, bayan su mutum daban daban muka tambaya suka kuma tabbatar da magana d’aya sunanki AYSHA… Sharif ya ce “Ka gani ko Ahmad? Shi yasa sam ba a yabon mace…” Da sauri na ‘d’aga masa hannu na ce “Ba ita bace Sharif, ba AYSHA ba ce wallahi sai dai idan wani coincidence d’in ne ya faru….” Sharifs ya girgiza kai ya ce “Haka ne Allah ya kyauta..” Ranar kam sai Shariff ne ya jani zuwa gida don bana jin zan iya driving a irin tashin hankalin da nake ciki, gashi a ranar za’a kai ki… Da yammacin ranar Mommy ta shigo cikin d’akina tana kiran sunana Ahmad me ke damunka ne?” Na girgiza kai na ina furta bakomai Mommy. Sai naga ta yi murmushi ta ce “Allah yasa bakomai d’in.” Wayata da take ta ringing na k’i d’agawa ta kalla sai naga ta saka hannu ta ‘d’au wayar ta ce “Ba kiranka ake ba Ahmad?” Da sauri na mik’a hannu zan amsa wayar sai ta ce “Ai ta ma mutu, yauwa bari naga vedion gidanka da ka ce ranar ka ‘d’auko jama’a basu bar ni na gani ba ance iyayen yarinyar sun yi k’ok’ari…. Ko kafin na yi wani yunk’uri naga Mommy ta waro ido ta ce “Ahmad me nake gani wannan kamar hoton matarka tsirara da wani mutum! 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA…. 43 NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Ganin idanun matar zube a kaina ya sa na gagara yi mata musu, a hankali na saka spoon na fara Shan romon da’din da romon ya yi ne yasa na shanye shi tas ba tare da sani na ba. Na d’ago ina kallon matar da take ta kallona tana sakin murmushi. Ta ce “Ko ke fa? Yanzu kinga Maminki zata ji kyakykyawan labari.” Ban amsa mata ba na mayar da kaina na kwanta saboda barci da na ji yana fisgata. Hakan yasa ita ma bata sake min magana ba, ban San lokacin da ta tafi ba sai tashi na yi naga bata nan. Na mik’e cike da kasala ina kallon Aunty Doctor da take tsaye a kaina tana min murmushi ta ce “Inlaw jiki ya yi kyau ko? Ma sha Allah hope ba inda ke Miki ciwo?” Na ‘daga kaina ina d’an sakin murmushi duk jina nake wani ido ga wata kunyar mutane da na tsiri ji, na San dai by now kowa ya San me na aikata. Ta dafa Kai na a hankali ta ce “Gaskiya jiki ya yi kyau, zuwa da safe zan sallameki Amma Akan shara’dai sosai, kada ki yi wasa da lafiyar ki,kada ki sake koda wasa ki sake yarda da shi sai nan da 2 weeks na San kafin nan jikin ki ya sake kyau, don haka a shawarce ma zan iya cewa Inna ku tafi da ita gida, ko a samu me zama da ita…” Inna da take gefe tana Shan tea d’inta. Ta gyara zama da sauri ta ce “Yo ni zaman me nake? Da ba zan bita can gidan na kula da lafiyar ta ba, ai dole na ne shi wannan wajen ai dole sai an bashi kulawa sosai don shine martaba da mutuncin y’a mace, ke dai likita Allah ya saka Miki da alheri.” Aunty Doctor ta amsa da Ameen tana sakin murmushi sannan ta saka Kai ta fita daga d’akin. Kashegari kuwa da safe aka sallamemu. Na dinga rok’on Inna Akan mu tafi can gidan mu Amma Inna ta kafe akan gidan Ustaz zata Kai ni, gidan da idan na tuna zan koma nake jin wani irin b’acin rai. Ban ce mata komai ba har Ustaz d’in ya shigo fuskarsa fal fara’a yana kallon Inna da ta gama parking duka Kayan mu a gefe. Yaya Usman ne ya shigo tare da matarsa hakan yasa na mayar da hankalina kansu. Ya.Usman yana kallon Inna ya ce Ashe an yi sallama?” Ta ‘daga kanta tana furta “Ai yau sai gida, ja’irar yarinya tun ‘dazu nake fama da ita Akan gidan mijinta zata koma, amma atabau ta k’i wai gidan Ubanta zata koma, gata nan Usmanu sai ka gaya mata ko zata ji.” Yaya Usman ya juyo yana kallona. Kamar yarda Ustaz ya yi cak shima yana kallona ta cikin idonsa na hango rashin nutsuwa da tashin hankalin da yake tattare da shi. Na turo baki ina kallon Yaya Usman da yake cewa Inna ai bata isa ba, dole a bi abinda mijinta yake so, idan shi ya amince ta koma gidan sai a k’yaleta…” Inna ta ce “Kuma fa haka ne, shine mai yanke zance, duk da ko gidan nasa ta koma ba tafiyar da zata tsinana masa, don likita ta jaddada lallai ya tsahirta mata idan ba haka ba d’inkin zai b’alle, don haka ina ga gwara kawai ya bari a tafi da ita can gidan Imamun….” Ina kallon Ustaz ya yi saurin sauke idonsa k’asa kafin ya fice daga ‘dakin na San kunya ce ta dame shi. Dariya na so yi ni kaina maganar Innan taso ta bani kunya amma ita ba abinda ya dameta ta juya ma gaba d’aya tana sake yiwa Yaya Usman bayani shi dai ina kallo shima ya fice da sauri na San bayan Ustaz ya bi. Bai wani jima ba sai gashi ya dawo. Yana kallon Inna ya ce “Ki k’yaleta ta tattara ta bi mijinta ai shi ba mahaukaci ba ne zai kula da lafiyar ta.” Inna ta kalleshi a kaikaice ta ce “A barta ta bi shi ita ka’dai kake nufi?” Usman ya d’aga Kai, Inna ta ce “Ah to wannan ne baku isa ba, idan yarinyar ta lalace Baku da asara ko? To k’afata k’afarta haba wa ina dalili wannan mijinnata da ko kunyata baya ji a gabana yake bata sumbata ko ya rungumeta yana zaton barci nake, shi kake cewa zai d’aga mata k’afa…” Usman shiru ya yi yana kallon matarsa ya ce “Bari na wuce dear, idan zasu tafi ki bi su ki ‘d’an taimaka mata da gyaran gidan.” D’aga Kai ta yi tana murmushi a hankali. Shi kuma ya fice. Bayan mintuna sai ga nurse ta dawo ta ce Ustaz ya ce mu fita yana jira a mota. Dariya abin yaso bani ta yarda duk rashin kunyar Ustaz yau Inna ta k’ure masa maleji. Suka d’ebi Kayan ni kuma na zura Hijab d’in da Ustaz kullum sai ya kawo min wani. Muka fita zuwa wajen mota. Aunty Doctor na tsaye da Ustaz a gaban motarsa ina kallo har mur’da masa kunne take yi da alama kashedi take sake jaddada masa. Na ga ya tab’e baki yana ganin mu ya yi saurin bu’de min gidan gaba na shiga. Su Inna suka shiga baya. Aunty Doctor ta mana sallama muka tafi. Karatu kawai Ustaz ya saka Amma cikin dabara sai da ya lalubi hannuna ya rik’e a nasa hannun yana murzawa hannu gudan kuma yana driving. Lokaci lokaci sai ya juyo ya kalleni ya saki murmushi ko ya murza hannun idan na juyo kawai sai ya lumshe ido ya ce “I LOVE YOU…” tsaki nake masa na d’auke ido na. Muna isa gida kuwa tas Auntyn Useey ta gyara gidan ta ‘dora abinci. Inna kuwa ta kasa ta tsareni a ‘dakina ta hana ni fita. Sai ga Auntyn Useey ta shigo tana k’unshe dariya ta mik’o min wayar hannunta da na tabbatar ta Ustaz ce, “Ana Miki waya.” Ta fa’da tana dariya ta fice. Wayar na kara a kunnena ina jinsa ya saki ajiyar zuciya Jin muryata ya ce “Ba zaki zo ba ko? Kin bi ta maganar tsohuwar nan?” Na turo baki a hankali na ce “Ba zan zo ba d’in, me zan zo na maka?” “Mhmn” Ya ce, kafin ya ‘dora da “Allah idan baki zo ba zan shigo yanzun nan na aikata abinda tilas Inna ta bar min d’akin…” Tab’e baki na yi na ce “Bismillah idan zaka iya” na kashe wayar na ajiye a gefe, abin haushin hatta da wayarsa k’amshin mayen turarensa da ya riga ya huda jikinsa take. Nocking na ji a hankali kafin na yi magana Inna ta ce shigo mana. Ya kuwa shigo sanye cikin shigar jallabiya sai walwali take da alama wanka ya yi, don na lura akwai soyayya mai kyau tsakaninsa da wanka. Y’a rusuna ya gaida Inna kafin ya tako zuwa bakin gadon gaba na sai fa’duwa yake ganin kamar da gaske yana shirin kunyatani a gaban Inna. Na waro idona ina nuna masa Innar da idona. Ya tab’e baki yana min nuni da ina ruwansa…. Inna kuwa ta zuba masa ido na San so take taga iya gejin rashin kunyarsa. “Tashi mu je za ku gaisa da abokaina Sun zo duba ki.” Ya fa’da yana mik’e min Hijab. Ina mik’ewa Inna ta mik’e itama tana kallonsa ta ce “Banda abinka Ahmad Ai da sai ka ce su shigo, tunda ka ga ai ba zai yiwu ta yi ta zurga zurga ba wajen bai gama ha’dewa ba. Mu je mu gaisa da su ita ta zauna kawai ba sai ta je ba…” Ina kallo Ustaz ya saka yatsa yana murza goshinsa kafin ya ‘d’ago ya ce “Yanzu zata dawo ai, kuma basa jin hausa idan kin je ba ba gane abinda zaki ce za su yi ba…” Inna ta ce “Ai hikkenan, sai ku je Amma dai ta dawo yanzun nan saboda a kiyaye dokar likita.” Ustaz ya ‘d’aga mata kai kawai yana saka hannunsa cikin nawa muka fice daga bedroom d’in. Tun a hanya na fara turje masa, ina turo baki na ce “Pls! Ustaz wai ina zamu?” Ya juyo ganin zan b’ata masa lokaci naga yasa hannu ya d’aukeni cak, ya haye da ni step d’in da zai kai mu ‘dakinsa. Bai dire ni ko ina ba sai saman gado, ya kalleni yana murmushi kafin yabi jikina ya kwanta ya rungumeni sosai yana sakin ajiyar zuciya. Zan yi magana naji bakina a cikin nasa sai da Ya yi son ransa sannan ya sake ni yana mayar da ajiyar numfashi ya ce “Ba abinda zan Miki matsoraciya barci kawai nake son yi a jikinki….” Hawaye ne ya kawo idona na ce “Kada ka sabawa kanka abinda ba zai d’ore ba, am serious ba zan zauna a gidanka ba, ka cika ni na koma kada Inna ta yi fa’da…” Bai cika ni ba sai ma sake shiga jikina da ya yi sosai ya ce “Kina sake magana kuma, zan canja mind d’ina na sake bu’de d’inkin can…” Shiru na masa ina jinsa yana wasu irin abubuwa a jikina Kafin barcin gaske ya d’aukeshi. Wayarsa da take vibrating ce tasa nima na farka daga barcin da ya fara fusgata ina kallon wayar naga an saka Hayateey sai kawai naji ina son sanin wacece don haka na kara wayar a kunnena ba tare da na yi magana ba. A zafafe na ji Mommy ta ce “Wato Ahmad ka Mayar da ni abokiyar wasanka ko? Wannnan ne dalilin da yasa fa da farko na k’i amincewa da auren nan don naga gaba ‘d’aya hankalinka na wajen yarinyar can son da kake mata ya yi yawa, to bu’de kunnenka ka ji Da kyau wallahi gobe sai kun tafi da Hameeda ba fashi idan Kuma ka k’i bin umarni na ban yafe maka ba, zan kuma yi sanadin da zan raba auren naku Har abad…” Ji na yi ya zare wayar daga kunnena ransa a b’ace ya mayar kunnensa yana Cigaba da sauraran Mommyn tasa… idanunsa kafin ya gama wayar sun ka’da sun yi jajir. A hankali ya sauke wayar daga kunnensa yana lumshe ido. Wani abu mai kama da tausayinsa na ji yana fisgata sai dai ban yi magana ba na d’au Hijab d’ina na zura da niyyar tafiya na ji ya rik’o hannuna da sauri na fa’da jikinsa. Bakina ya kama da k’arfi yana kissing cikin wani irin yanayi. Bai daina ba har sai da leb’ena suka yi jajur sannan ya saki murya a raunane ya ce “Wa ya ce ki d’aga min wayata K’alb?” Na turo baki na ban yi magana ba. Sai na ga ya saki murmushi ya ce “Am…na San kinji abinda kike so ki ji. Fine…” Ya fa’da yana murza goshinsa a hankali ya mik’e daga gadon gani na yi ya d’auke ni cak mun shiga wata k’ofa sai a lokacin na tabbatar toilet ne. Da sauri naja na tsaya ina furta “Me.. Me zamu yi anan?” Ya lumshe idonsa a hankali ya furta “Love bathing….” Ya fa’da yana bu’de jirkitattun idanun cikin nawa. Na waro ido ina furta “Ni a’a…” Matsowa ya yi daf da ni ya ce “Pls! K’alb, mu yi ko don na dinga tunawa da ke, kin dai ji Mommy ta ce tilas mu tafi da Hameedah gobe kuma na San zan iya kaiwa 8weeks ban dawo ba, ban san yarda zan yi da rashin ki ba, gashi sau ‘d’aya na yi tasting amma kin zautar da ni. Ko da yake ina zuwa zan fara Miki processing Visa kema ki biyo ni…” Tab’e baki na yi na ce “Allah ba inda zan bika, ai yanzu ma na sake jin aurenka ya fita daga raina tunda Babarka bata sona, ba zan zauna a inda ba’a so na ba na San ko nan gaba wahala zan sha, don haka dole kafin ka tafi ka sake….” Ji na yi ya jani jikinsa ya ha’de bakinsa da nawa kafin na ce komai sai jina na yi a cikin bathtub da ya cika da ruwa, ranar kam ni Naga wanka a wajen Ustaz duk da bai yi min komai ba amma jikina ya wahaltu. Da kansa ya sauka sai ga kaya ya taho min da su. Ina kallonsa kamar na yi kuka na ce Inna fa?” Ya tuntsire da dariya ya ce “Tana can tana barci, Allah dai ya yiwa matar Usman albarka da ta kawo idear saka mata maganin barci…” na waro ido ya d’aga min gira yana sake jana jikinsa a kunne ya ce min “Yau kin sake gigita ni da surar jikin ki Eehsha! Anya nan gaba akwai wata macen da zan sake yiwa kallon mace…” “Har ita y’ar mutuncin da ta San martabar iyayenta….” Goshinsa ya goga da nawa ya ce “Har ita Eehsha, Har kowa ma ke ta daban ce a cikin mutane na daban…. Na tabbata a cikin mata dubu da k’yar a samu biyar irinki, Wai Zuma kenan…” Turesa na yi ina tab’e baki na yi nufin sauka ganin yarda lokaci ya ja. Ina ji ya saki ajiyar zuciya ya ce saura dare zan zo d’aukan ki mu yi bankwana….” Tsaki na ja a hankali na ce “Wallahi kada ma ka fara…” ina ji yana dariya na sauka a hankali. Gidan shiru da alama Auntyn Useey ma ta tafi. Ta dafa mana abinci kuwa na lek’a ko ina ban ganta ba sai takardar na gani akan dinnig ta yi rubutu ka’dan. Ki yi hak’uri AYSHA Yayanki yazo mun tafi a sha amarci lafiya na tausayawa Ustaz ne shi yasa na taya shi samun abinda yake so..” Na yi k’wafa na yaga takardar na cilla dustbin kafin na tura k’ofar cikin d’akin. Inna ce ta motsa a hankali ta mik’e tana kallona ta furta “Kin dawo kenan?” Na gode da addu’oinku da masu waya yi min gaisuwa da masu zuwa jazakumullah Khaira Jaza’ihi. Allah ya bada lada Allah ya ji k’an mamatanmu ya kyautata namu zuwan. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA…. 41. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Kallonta nake kawai kamar yarda Umma ma ta zuba mata ido ganin yanayin kallon da take mana kamar taga wani abin k’i. K’anwarta kuwa da fara’a ta tareta tana furta “Aunty ke ce da safiyar nan, Yanzu haka Ahmad ne y’a d’addako ki kamar a kansa aka fara aure duk yabi ya tayyara yarinya, ina ji dai kaf dangi yau ba Wanda ba zai San matar Ahmad ta kawo budurcinta ba, rashin kunyarsa wallahi har mamaki ta ba ni.” Ido na runtse da sauri jin abinda k’anwar take fa’dawa yayarta. Yak’e kawai Mommyn ta yi tana duban Umma da k’yar suka gaisa. Ina daga kwancen nima muryata a k’asa na ce “Ina kwana Mommy.” Ta ‘dan yi murmushin da na tabbata bai kai k’asan zuciyarta ba ta ce “Ya jikin?” Ban amsa ba sai Aunty likita ce na ji ta ce “Wannan jikin nata ai ba wani sauk’i, ina ji dole na tattara ta na tafi da ita asibiti.” Mommy ta yi shiru kafin muga ta mik’e ta fice daga d’akin. Tsawon mintuna d’aya itama Anty Doctor ta bi bayanta. Hakan yasa na rage daga ni sai Umma a bedroom d’in. Umma fara’a fal fuskarta ta k’araso inda nake ta zauna a gefe na murya a k’asa ta ce “Alhamdulillah AYSHA, yau dai kin kankaro mana martaba da mutuncin mu, Ubangiji Allah ya Miki albarka, ashe duk zargi da zaton da ake Miki ba haka ba ne, a yanzu Abbanki ya yarda ai ya tashi tsaye a tsaurara bincike a gano musabbabin wancan gantalallen vedion.” Ni dai runtse ido na nake kawai, saboda azabar da nake ji a gaba na, ga zuciyata ita ma suya take, menene ban gayawa Umma ba Amma ta k’i saurarata. “Ki yi hak’uri AYSHA In sha Allah yanzu zaki samu sauk’i, ki yi ta addu’a ni ai wannan ciwo ina maraba da shi, saboda irin ciwon da ake so ne, da k’arfin zuciyata zan ta sanar da dangi baki da lafiya don kow ya san kin kawo budurcin ki d’akin Mijinki. Inna zan fara gayawa yanzu don na San ita zata kwaza kowa ya ji, ce mata zan yi tazo ta yi jinyarki baki da lafiya idan tazo sai taga komai da idonta…” Kallon Umma nake kawai ina mamakin abinda take fa’da kunya kuwa ta yi min rufdugu, ita yanzu ba zata ji kunyar terere da wannan al’amarin ba. Shigowar Aunty Doctor da Mommy ne ya saka Umma yin shiru sai dai fara’a da walwalar fuskarta sam ba su d’auke ba. Mommy ta d’an kalleta kafin ta ce “Hajiya ni zan wuce Allah ya bata lafiya, za ku je asibitin yanzu da Tasleem.” Umma ta ce “A’a, nima ba Dani za’a ba, zan koma gida na turo wacce zata zauna da ita, tunda ta ce zata kwana biyu a can.” Mommy ta d’aga kai kawai tana wani shan k’amshi ta fice daga ‘dakin. Umma ma ta mik’e suka kama ni da Aunty Nurse suka fice da ni zuwa wajen motocin. Ustaz dai kasa fitowa ya yi ba mamaki kunyar Umman ce ta saka ya kasa fitowar. Driver yana jan motarsa da Umma a ciki. Ustaz ya fito daga inda ya b’oye. Hararar gefen ido na wurga masa ina jin zafinsa da haushinsa cikin raina. Shi kuwa da murmushi fal fuskarsa ya wani dafa ka’ina ya ce “Ya aka yi K’alb, hope kina samun sauk’i yanzu?” K’aramin tsaki na ja a hankali, Wanda Ustaz d’inne kawai ya san tsakin na masa. Murmushi ya yi ya d’an yi kissing leb’ena na lura sam Ustaz ba ya jin kunyar Aunty Tasleem ko don ya sa’ar ce oho masa. Bata masa magana ba illa harara da ta wurga masa ta ce “Zaka shiga mu tafi ne ko kuwa zaka tsaya rashin kunya, ina ma ban bawa Khala hak’uri ba ta tattaraka ta saka dole ka bi matarka wallahi.” Ya d’an waro ido ya ce “Ai kuwa Allah da ba zan iya ba.” Ta d’an yi k’wafa ta na fara driving ta ce “Kada dai ka yi breaking promise da ka d’auka, nextweek ka ce zaku tafi don haka ba fashi, ka ji na gaya maka.” Ya d’an tsuke fuska yana d’auke kansa bai yi magana ba sai dai ya ja hannuna ya rik’e gam kamar wani zai k’wace masa ni. Sanyin a.c da k’amshin turaren Aunty Tasleem ne yasa barcin da nake ji ya rinjaye ni, Har ban san mun isa asibitin ba. Sai da naji Ustaz ya birkito ni jikinsa ya manna min kiss a goshi da tsinin hanci na sannan na bu’de ido da sauri ina kallon gaban motar sai naga ba k’anwar uwar tasa a ciki. Ajiyar zuciya na saki kafin na yi k’ok’arin Zare jikina, amma bai ba ni damar hakan ba, a kunne ya ra’da min “Bari mana, yau kam ai na zame Miki magnet wallahi, ni ka’dai na San duniyar da kika wulla ni jiya. Mai kike so na baki ki fa’da ko meye Allah zan baki.” Ban masa magana ba muka ji an k’wank’wasa k’ofar na yi saurin ture hannunsa daga cikin rigata ina gyara hijabi na. Bai sake ni ba sai da ya manna min sumba a lab’b’ana sannan ya bu’de k’ofar motar bayan ya saka black shade a fuskarsa. Ba Doctor ba ce wasu nurses ne matasa suka kama ni suka fito da ni daga motar aka saka ni a wheel bed kamar wacce na ce musu ba zan iya tafiya ba, duk tafiyar da k’yar nake yinta, k’afafuna kamar duk kaluluwa ne a jikinsu tsabar ciwon da suke min, hakan da suka min tabbas ceto na suka yi. Ustaz yana daga gefe yana ba su umarnin su tura a hankali kada su yi sauri. Duk abinda yake sam baya burge ni don na k’udiri niyyar sai na rama abinda ya min ba abinda zai saka na zauna da aurensa…” Wani ‘daki mai kyan gaske aka kai ni aka shimfi’dar akan gado. Doctor ta shigo da kayan aiki. Tana kallon Ustaz ta ce “Dole a mata d’inki ko yaya ne? Saboda abinda ka mata bana tunanin Wanda yake cikin hankalinsa zai aikata…” sunkuyar da kai ya yi yana sosa k’eyarsa. Ni kuwa jin wai d’inki za’a min sai da gaba na ya fa’di sosai, na shiga wuri-wuri da ido. Ganin ina shirin wahalar da ita a wajen allurar kashe waje ma kawai hakan yasa ta kalli nurse d’aya ta ce “Kira min Doctor Musa, ina ga dole sai ya taya ni ba zata tsaya ba.” Wani irin kallo Ustaz ya mata yana furta “Me? Wani k’aton kike cewa yazo yaga min sirrin matata?” Tasleem da dariya taso kufce wa ta kauda kanta tana furta “To me zai gani a jikin matar taka? Jikin mata nawa ya gani kafin natan?” Ustaz ya cije bakinsa ya ce “Kada ma ki fara, ki bari zan rik’e Miki ita ki mata ke kanki a dole nake bari kike ganin wannan wajen da bana jin akwai abinda nake so sama da shi a rayuwata…” ta zaro ido tana masa kallon mamaki. Kafin ta ce “Lallai Boy ka San mace…” Sai kuma ta yi dariya shi kuwa sake tsuke fuskarsa ya yi yana furta “Kin san dai bana son sunan ko?” Ya taso ya hau gadon sosai bayan ya ce yaran nurses d’in su matsa can gefe. Ya jani jikinsa sosai a tsakiyar k’afafunsa da ya warasu sannan ya wara tawa k’afar. Zuwa lokacin na rage jin tsoro saboda allurar ta fara bin jikina, ban ma san me take ba har sai da ta gama sannan ta kalli Ustaz ta ce “Ga shi nan na gama mata ban gutsire ta ba. Sai ka tashi a gyara mata kwanciya. Duk bala’in ka kuma ka bar yarinyar mutane ta warke ras. Ka tattara komatsanka ka tafi da Hameedah.” Daga haka ta fice ni kuwa tuni na runtse ido na don bana son Ustaz ma ya san ido na biyu. Ya ‘dan rankwafo ya gyara min kwanciya. Yana sumbatar forehead d’ina. Cikin husky voice ya furta “Ana Uhubbika katheer katheer… turo k’ofar da aka yi ne ya saka shi saurin ja da baya yana amsa sallamar. Nima na d’an bu’de ido na Jin muryar Babar su ZINATU ce. Ta k’araso fuskarta ba yabo ba fallasa take amsa gaisuwar Ustaz da yake sunkuyar da Kai. “Ya mai jiki kuma? Wai me ya sameta ne?” Ustaz murmushi kawai ya saki ina kallo ya fice daga d’akin. Cikin muryar basarwa na gaida Umman ZINATU ta d’an kafa min ido daidai lokacin da Anty Khadija ta turo k’ofar ta shigo itama. Ta yi saurin k’arasowa tana furta “Sannu Aysha, ni yanzu Yayanku ya min waya ya ce nazo asibiti an ce baki da lafiya.” Na d’aga mata Kai na. Ta ce “Subhanallah, me ya sameki haka?” Ban amsa mata ba Doctor ta shigo tana kallonsu suka gaisa sosai sannan ta ce “Waye mai zama da ita?” Umma ZINATU ta ce “Ni ce, kafin gobe kakarta tazo daga potiskum wani abin ne?” Doctor ta girgiza Kai. Ta ce “Bakomai ba ne, kawai dai ana son a kula da ita sosai, kin San idan mutum ya samu issue na d’inki akwai buk’atar a kula da shi sosai ko don gudun samuwar infection, a dinga shiga ruwan d’umi mai d’an gishiri ka’dan.” Umman ZINATU da mamaki a fuskarta ta ce “D’inki kuma? Subhanallahi me zai jawo mata d’inki kamar wacce ta haihu?” Doctor ta saki murmushi ta ce “Ana samun irin haka sosai ga budurwar da namiji ya fara kusantarta a Daren farko, Allah dai ya bata lafiya, ni zan wuce Aysha idan da matsala ki fa’da ma Ustaz sai ya kira ni.” Daga haka ta fice ta bar Umman ZINATU da hagamemmen Baki, ita kuwa Anty Khadija cikin farin ciki ta ce “Alhamdulillah Allah mun gode maka Aysha kin bawa munafukai kunya, yanzu kuma kowa ya San ba kya yawon banza a daina yama’d’idi da zancen…” ni dai murmushi na yi a zuciyata ina mamakin anty Khadija da Sam bata Jin kunyar fa’dar gaskiya a koda yaushe. Ita kuwa Umman ZINATU shiru ta yi duk fuskarta ba walwala. Haka aka fara zuwa dubiya duk Wanda yazo kuma Anty Khadija bata Jin kunyar ta sanar masa budueci na Kai gidan Ustaz shi yasa na samu raunin da aka min d’inki, ita take fa’da ni take bari da Jin kunya. Har dare ban sake ganin Ustaz ba, tunda ya lek’o yaga jama’a da yawa a d’akin, bai shigo ba ya fice da sauri. Ya dai kira Anty Khadija ya ce ta bani wayarta ta. Ya tambayi ba abinda nake so, shiru kawai na masa maganar duniya na k’i amsa masa, k’arshe dole ya yi cutting wayar. Ni kuwa na bi wayar da harara kamar Ustaz d’in ne ya zama wayar. Yayyena maza ba Wanda bai zo ba, fuskonkinsu cike da fara’a sai dai ni kuma ba Wanda na kula sai Yaya Useey. Da daddare sai ga Abba na a idonsa na hango irin tsabar murnar da zuciyarsa take ciki, duk da bai yi min magana ba, amma irin kayayyakin da ya judo ya kawo asibitin Sun tabbatar min da hakan. A hankali kuma ya ce “Allah Miki albarka 𝑨𝒚𝒔𝒉𝒂𝒕𝒐𝒖, wancan lamari kuma ki bar damuwa in sha Allah zan yi bincike mai tsauri a Kansa.” Shima ban amsa masa ba shiru kawai na yi. K’arfe 9:00 Ustaz ya shigo, cikin wata azababbiyar Jallabiya coffee color Kansa ba hula hakan ya bawa kwantacciyar sumarsa damar fitowa sai k’yalli take. Kamar yarda sajensa da gemunsa suka kwanta suka yi luf. Wani irin k’amshin turare kake ji kawai a d’akin. Ta gaishe da Umman ZINATU har k’asa. Sannan ya k’araso wajena. Ba mamaki Umman Zinatun kunya ta ji ta mik’e da sauri ta fice bayan ganin Ustaz ya zauna daf da ni a gefen gadon yana kama hannuna. Murmushi ya yi ya bi bayanta da kallo a hankali ya mayar da idonsa kaina ya ce “Na koreta, na San idan ba haka na mata ba ba zata bari na sake da ke ba, ni kuma so nake kawai….” Sai na ga ya kanne ido yana d’aga gira yana kallon boobs d’ina. Tsaki na yi ina k’ok’arin gyara zama na, ya ce “Kada fa ki tashi, k’in ci abinci bari na kira Aunt Tasleem ta duba ki.” Na wurga masa harara na ce “Kai wai baka Jin kunya ne?” Ya yi dariya yana d’an sosai gefen hancinsa ya ce “Kunya for what reason zan ji kunya? Ai ni haka nake so ko ya San dal na b’are Eehsha a leda.” Na turo baki na ina furta “Ai shikkkenan ka ji da’di. D’azu ka ce na gaya maka duk abinda nake so zaka min, da gaske kake ka yi alk’awari?” Y’a d’aga Kai yana Jan karan hanci na ya ce “Gaya min koma me ye zan maki ko zan siya Miki koda duk arzikina za su k’are….” Na yi murmushi ina d’an Jan fatar leb’ena na cija ka’dan, ban Kai ga saki ba sai kawai na ji Ustaz ya saka bakinsa a nawa yana bani deep kiss. Ya yi son ransa kafin ya sake ni yana mayar da numfashi idonsa a lumshe ya ce “Ai sai ki ce min Ustaz I need you…” na ware ido na ce “Haka na ce maka?” Shima narkakkun idonsa ya shigar cikin nawa ya ce “Haka inkiyar ki ta nuna min, oya tell me, me kike so kuma, I promise you zan Miki yanzun nan.” Cikin idonsa na kalla murya ta a sark’e kamar mai mura na ce “Ustaz I want divorce right now…….saki kawai nake buk’ata yanzun nan, kuma kada ka manta muhimmacin cika alk’awari a musulunci….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….42. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Wani irin tashin hankali na gani kwance a cikin idanunsa, Har idanun ya fara tara k’walla. Hannunsa shaking yake a cikin nawa hannun sosai. Ya dinga kallo na yana cije leb’ensa. Har kallon ya isheni na janye nawa idon ina jin a zuciyata abinda na zartar d’in Shine daidai bana sonsa a yanzu ba kuma zan iya cigaba da zama da shi ba. Abinda nake so a gane an gane to kuma me zan yi? Ai yanzu nawa wasan zai fara. “Eehsha!” Ya fa’da cikin rawar murya yana dawo da fuskata saitin tasa fuskar. “Ki kalle ni pls, I want to talk.” Na k’i kallon nasa don ban shirya ya karyar min da zuciya ba. Inaga ganin ba zan kalleshi d’in ba ne yasa ya matsa hannu na a hankali ya furta “Please kada mu yi haka da ke K’alb, wallahi ba zan iya ba, zuciyata zata raunana Kada kice zaki min ramuwar gayya ta wannan hanyar wallahi ba zan jure ba AYSHA ko magagin mutuwa nake ba zan iya furta Miki kalmar saki ba….” Na ware ido na ina kallonsa kafin na saki murmushi da shi da kansa na San ya san na rainin hankali ne na ce “A yanzu ne ba zaka iya saki na ba kenan? Da ka tabbatar ni ba karuwa ba ce, mai yasa wancan lokacin ka sake ni alhali ba wuk’a aka saka maka a mak’oshi ba, wallahi Ustaz sai ka sake ni don na ci alwashin ba zan zauna da kai ba, I hate you Ustaz! Na maka tsanar da bana jin ina yiwa wani abin halitta ita….” Gani na yi ta runtse idonsa da suka yi jajur ya ce “Baki yarda da abinda na ce Miki ba kenan, wallahi Mommy ce ta tilastani wancan sakin ma ba son raina ba ne…” Na janye hannuna ina tab’e baki na ce “Ina ruwa na kuma, kai da Mommyn kuka jiyo kuma ku ta matsewa ni dai wallahi sai ka sake ni don daga nan ba zan koma gidan ka ba.” Da sauri yasa hannu ya rufe min baki yana furta “Shshhhh, kin san Allah ba ya son mace ta ce mijinta ya saketa hakan illa ce a wajenta wallahi don mala’iku tsine mata suke…” “Haka nan Allah ba ya son saki don Al’arshi girgiza yake idan an yi sa, don haka da ni da kai duka masu laifi ne wajen Allah tunda ban maka komai ba sai zalunci ka sake ni ranar da na tare a gidanka akan zargin da baka tabbatar ba, to wallahi a yanzu nima sai ka sake ni ko na maka ka a kotu….” Bakina ya bi da kallo yana d’an sakin murmushi ba mamaki ganin yarda bakin yake tsiwa yake ko kuma ya d’auki magana ta wasa. Don haka a zafafe na ce “Wallahi d a gaske nake, ba mai saka ni na canja abinda na yi niyya…” Ya mik’e tsaye ya ‘dan rankwafo da kansa saman fuskata ina jin hucin numfashinsa ya manna min kiss a lab’b’aina duk k’amshin turarensa ya bi ya baibayeni… “Har abada ba saki a auren mu, wancan ma k’addara ce aure na da ke Mutu ka raba ne Madam….” Na ce “ko?” Ya d’aga min gira yana lumshe ido. Na yi k’wafa na ce “Za mu gani.” Dariya ya yi ya sake manna min deep kiss a goshi ya ce “Mu ga alheri, na lura rigima kike ji bari na tafi ga wayata zan kira na dinga jin lafiyar K’alb…” na wurga masa harara bai bi ta kai na ba ya shafi kumatuna da inda ya tsole masa ido ya fita da baya da baya yana blowing min kiss… yana fita naji wani hawayen takaici ya zubo min haushinsa nake ji sosai a raina, musamman auren can da ya yi na tabbata yanzu ma can wajenta zai je, a hankali na ja tsaki na furta “Mayaudari kawai, mai k’aton kai…” sai kuma na saki murmushi ni ka’dai ganin yarda Ustaz yake neman saka ni na zauce. Umman Zinatu ce ta shigo don haka na ja baki ja tsuke don bana son mata magana sam, na lumshe idona kamar mai barci ina ji tana furta “Ba dai barci kika yi ba tun Mijin naki bai tafi ba.” A zuciyata na ce “Almunafuk’ati ban sani ba.” Tun biyun dare ya dinga kirana a wayar ina ignoring d’insa. K’arshe don dole na d’aga wayar ganin ba zai bar kira na ba. Ina ji ya saki wata ajiyar zuciya, ya furta “Na kasa barci K’alb.” Zuciyata a tunzire na ce “Ko? Me zai hana ka barci bayan ga ka ga matarka….” Ina ji ya katse wayar bayan ya yi dariya sai kuma ga kiran vedio call ya shigo. Haka kawai na ji ina son sanin a inda yake wata ballagazar mata ce mai barin mijinta waya cikin dare… na d’aga kiran sai na ganshi a d’akin da muka sha budiri jiya. “Kin ganni, rungume da rigar barcinki mai d’umbin tarihi a wajena sai shinshinar k’amshin turaren jiki nake amma ya kasa kawar min da feeling d’in da nake ji a raina. Jikina maha’dinsa kawai yake buk’ata, ga Tasleem ta ce sai na baki koda 1 month ne kin warke sosai…” k’aramin tsaki na ja, ganin yarda yake wayar jikinsa ko riga babu sai wani lumshe ido yake. “Ka koma wajen matarka mana.” Ya d’an bu’de ido yana kallo na ka’dan cikin wata irin murya ya ce “Eehsha, are you jealous?” Na zabga masa harara na ce “Allah ya kiyaye na yi kishinka, kawai shawara na baka ko ka manta ita ce y’ar mutunci, y’ar gidan mutane masu mutunci ba ni da na watsar da martaba da mutuncin iyaye na a idonka ba….” Ina kallo ya runtse idonsa ya na jijjiga kai kafin ya yanke kiran. Sai ga msg d’insa ya shigo. “Idan na zo gobe, I will explain to you clearly…” na yi tsaki na cillar da wayar… ina jin haushin Ustaz ne zai kashe ni, zan jira gobe na ji da wace k’aryar zai zo… Kashegari around 10:45 Inna ta shigo asibitin kallona kawai take tana murmushi kafin su gaisa da Umman su Zinatu, Inna bata yi shiru ba sai da ta ce kuma Laraba sai al’amari ya canja, wancan labari duk k’anzon kurege ne, ai kuwa Ubanta ya ce ba zai yarda ba tunda ya tabbatar sharri aka ma y’arsa ba abinda zai hana shi d’aukan mataki, kuma nima ina bayansa Eehe, ba kunyar da baa saka ni cikin ta ba, musamman a k’aramin gari irin potiskum Allah ya tsinewa Wanda ya ha’da wannan kirumurmura…” Shiru Umman Zinatu dai ta yi kanta a k’asa ta kasa komai, sai da Inna ta yi son ranta sannan ta ce “Ai yaran yanzu ba wai lallai sai an kawar musu da budurci ba, suna soyayyar shan minti Allah dai ya shirya mana kawai…” Inna ta watsa mata wani kallo kafin ta furta “Laraba, na ga ba alheri ne ya kawo ki asibitin nan ba, sai tsabar sharri to ha’de kayanki tsaf ki bar nan wajen, tunda nema kike dole sai kin lalubo sharrin da za ki lik’a mata.” Umman Zinatu kamar jira take ta yi saurin fara ha’da karonta ta yi mana sallama murya a cunkushe ta fice Inna ta ce Allah ya raka taki gona dama tun tana yarinya uwarta ke fama da ita akan rashin fa’dar alheri… ki ga shan minti akan ki da zuri’arki muguwar banza da wofi kawai. Ta gyara zaman ta tana kunce k’ullin da ta zo da shi. Flask ne ta bu’de sai ga kunun gya’da mai zafi ta zuba min a cup d’aya kwanon kuwa chicken pepe soup ne da ya sha kayan k’amshi ta zuba min ta cika bowl da shi. “To maza tashi, irin wannan lalurar sai an tashi tsaye da gyara idan ba haka ba ki zama lusarar mace kina ji kina gani zaki dawo salaf ba ‘dand’ano ko ka’dan kamar kaza na dafa ta ba maggi, ah to ni dai ba ruwana sai an dage haik’an da gyara da cima mai kyau sai ki ga wajen da ya raraka ya dawo.” Na mik’e a hankali na karb’i bowl d’in da cup na fara shan kunun dama ni na San Inna ba k’aramin iya girki ta yi ba. Ina cikin sha sai ga Ustaz ya shigo k’amshinsa gaba d’aya ya gama mamaye d’akin, duk da hassada ta ba zan k’i fa’din ya yi kyau ba, cikin black jallabiyar da take ta shinning kansa ba hula sai hirami da ya saka a kan ya d’an yafa shi kamar yafen d’an kwali. Kallo na yake yana murmushi kafin ya mayar da hankalinsa wajen Inna da yake zaune tana lazimi tana gyangyad’i. Da sauri ta kalleshi kafin ta amsa gaisuwarsa ganin ya zauna saman gadon da nake daf ya ja hannuna yasa ta mik’e tana fa’din “Rasa kunya, kai yaran Zamani sai dai fatan shiriya…” Shi dai murmushi ya saki tana fita kuwa ya kwantar da kansa a jikina yana murmushi ya furta “I really missed you Baby.” Na tureshi ka’dan fuskata a yamutsa na ce “Ni fa ba matarka ba ce, ta mai rabo ce.” Sai jin lips d’insa na yi kan nawa yana gurza son ransa kafin ya d’ago na turo baki na ce “wace irin mugunta ce wannan da zafi fa.” Ya lumshe idonsa sai da ya kai bakinsa kunnena sannan ya ce “Bana son na ji an k’ara maganar sakin nan K’alb, kin san me yasa na dinga jingina ki da wa’dancan maganganun bakomai ba ne kawai don Naga reaction d’inki, anan zan gane za ki aikata ko baki aikata ba, Alhamdulillah irin yarda kika dinga nuna b’acin ranki a fili idan na fa’da Miki magana ya tabbatar min baki aikata ba…” “ko?” Na ce masa ina turesa daga jikina ya ‘d’aga min kai yana saka hannu ya amshi cup d’in hannuna ya kai bakinsa gani na yi ya lumshe ido ya ce “Ma sha Allah.” Na yi tsaki na ce “Ka ajiye duk abinda za ka ce ba zasu yi tasiri a wajena ba, da gaske saki nake so…” Shiru ya yi yana cigaba da Shan kununsa bai kuma damu ba don sai sakin murmushi yake. Har ya gama sha tsaf ya mik’e yana lakace min hanci ya ce “Rigimaty, Am leaving, don naga yau a kusa kike bari na tafi Neman na kai, ki adana rigimarki ba yanzu ba sai second night, ban sani ba ko a lokacin zata Miki amfani…” Daga haka ya bani feck a kumatu ya fice da baya da baya kamar yarda ya Saba. Lumshe ido na na yi kawai ina murzar goshi na a zuciyata kuwa tunani nake Ustazu ya gama mayar da zancena wasa. Ana idar da Sallahr azahar, Inna tana zaune tana lazimi muka ji nocking na amsa da k’yar da cewa Come In… Matar ta shigo sanye cikin dogon hijabi fuskarta sanye da nik’ab. Kallo na bita da shi ina son sanin wacece. Har ta iso gado na bata cire hijabin ba bayan ta gaishe da Inna da itama ta bita da ido. Sai da tazo bakin gadon nawa sannan ta d’aga nik’ab d’in. Ta d’an sakar min murmushi. Da k’yar na mayar mata don ban Santa ba, kamar ta shiga zuciyata sai Naga ta ajiye kwandon abincin a gefena ta ce “Ga sak’on da na kawo na San baki sanni ba, bari na baki wayar ki ji wacce ta aiko ni.” Ta latsa wayarta sannan ta kara min a kunne, muryar Mami na na ji tana furta “𝑨𝒚𝒔𝒉𝒂𝒕𝒐𝒖, ya jikin? Ga sak’o nan na bayar a kawo miki, ki tabbata naman ke kika cinye ko romo ba’a san wani ya lasa, shi yasa na sako a roba daban pls kada ki wasa da shi zaki gan shi a roba mai blue murfi d’aya mai Jan murfin kowa ma zai iya sha, ki kula sosai Allah ya bada lafiya…” Kafin na ce komai ta katse wayar. Jiki na na rawa na kalli matar da ta bu’de basket d’in ta Ciro exactly robar da Mami ta ce ta saka min a cinya a hankali ta ce “Maza ki cinye, don umarni ta bani kada na matsa ko nan da can sai kin gama tas, na tafi mata da robar….” Jikina ba inda ba ya rawa duk na shiga ru’dani…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ A yi hak’uri Kakata ce ta rasu, shi yasa gobe da jibi ba zan yi Posting ba wannan ma don kada ku ji shiru ne. Kuma already ina da shi a k’asa. Na gode sosai da adduoinku gareni Allah ya saka da alheri👌 [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: Wani irin Sarawa kaina ya yi, sarawar da na ji shi Har tsakiyar k’wak’walwata na runtse idona ina jin jiri na d’ibana. Tunani na guda menene wannan yaushe na aikata wannan abin da ko a mafarki ban san zan iya rik’e bindiga ba. Amma yau gani dumu dumu rik’e da bindiga. Kasa motsin kirki na yi don bani da k’arfin da zan iya motsa koda gashin idona ne balle wata gab’a ta jikina. Ina ji suka sanya min hand cuffs suka tasa k’eyata zuwa motarsu ta shiga ba biya fita da Allah ya isa. Da jiniya sosai muka bar cikin harabar gidan. Tuni zuciyata ta cunkushe waje guda. Bana iya tunanin komai sai na dama Allah ya d’au raina na huta da irin wannan rayuwar daga wannan masifa sai wannan, me yasa? Ni dai na San koda wasa bani ba ce a jikin Hoton nan Amma na San ko zan Mutu ina rantsuwa ba yarda za’a yi ba. Tsabar tashin hankalin da nake ciki yasa ko k’walla babu a idona illa iyaka idanun nawa Sun fito waje. Muna zuwa Office d’in y’ansanda suka tasa ni a gaba da tambaya. Tambayoyin da suka dinga saka zuciyata wani irin harbawa da k’arfin gaske. Har ban San sanda na runtse idona na furta “Ko ke ake tuhuma ta ni na aikata a yi min hukuncin da ya dace…” Tsit station d’in ya yi ina kallon Yaya Usman da su Abba suka runtse idonsu. Sam ban damu da tashin hankalin da suka shiga ciki ba damuwata a yanzu bata wuce ta barin duniya ba. Na gaji da rayuwar gaba d’ayanta. Dpo ya k’ura min ido ya ce “Kika ce ke ce kika aikata?” Na d’aga kaina kawai ba tare da na yarda na kalleshi ba. Ya ce “To ina sauran y’an uwa naki su bakwai da aka ce tare kuka aikata?” Na datse leb’ena da k’arfin gaske na ce “Ban San inda suka tafi ba…” ina kallo ya yi rubuce rubucensa yana kallon wasu y’an sanda mata guda biyu ya ce su je da ni su tuhumeni sosai na fa’di inda sauran y’an uwa na suke. Suka kuwa ingiza k’eyata muka tafi. Tambayar duniya da izayar duniya ba wacce basu min ba Amma na ce ban San inda suke ba. To ina zan sani tunda su kansu ban san su ba, asalima ban tab’a ganin fuskarsu ba, ban sani ba ko Aljannu ne suke siffata su aikata son ransu. Ba yadda za’a yi na yarda Biladama ne, saboda idan ana kwaikwayar fuskar mutum, ba ta yarda za’a yi a kwaikwayi komai da komai na jikin mutum ace hatta da farce ba banbanci. Abu d’aya da na tambayi kaina, me na yiwa Wanda ya min wannan sharrin da yake son ganin baya na? Aka ajiyeni a cell cikin kyakykyawan matakin tsaro da ba a barin kowa ma ya ganni. Ina ji Dpo na yiwa Abbana bayani “Alhaji ba Wanda zai sake ganinta sai ranar shari’a, ku nemar mata lawyer kawai.” Ina kallo Abba da Yaya Useey suka saka hannu suka share k’walla suka bar wajen. Na ji wani irin Abu ya tsaya min a mak’oshi. Tun daga ranar kuwa ban sake ganin kowa ba har tsawon kwana uku kafin zuwan lokacin kuwa na ji gata sosai, jigatar da ta bayyana har a saman idona. Ranar ina zaune a d’akin mai duhu sosai na dinga Jin murya kamar ta Ustaz tana dumfaro d’akin. Ina Jin muryarsa sama sama yana furta “Wallahi, idan ba’a sameta da laifin komai ba, sai na yi shari’a da Dpo d’inku… matata za’a tozarta don wulak’anci kuma ance mutumin da ake zaton an kashe d’in ma bai Mutu ba, to saboda me ba zaku saketa ba?” Ban ji amsar da wancan ya basa ba, naga dai an bu’de k’ofar Ustaz ya shigo tun daga fuskarsa har gangar jikinsa Sun bayyana tsagwaron tashin hankalin da yake ciki. Idanunsa tuni suka ka’da suka yi jajur. Ya fara cizon leb’ensa yana k’arasowa inda nake, ya zube a gabana murya a sark’afe ya ce “Ke ce a haka K’alb?” Kuka yake sosai ya kama hannuna ya ce “Sai jiya labari ya isar min wai an kulleki a station, how come Aysha da gaske ke ce a jikin hoton?” Na runtse idona tunda abin ya faru sai lokacin naji kuka yazo min Amma na yi dakiya na share na k’i kukan muryata a raunane na ce “Idan ka yarda nice a Hoton shikkenan ba abinda zan ce sai ni na aikata su yi min abinda ya dace Ahmad…” Murzar hannuna kawai yake ya kasa furta komai sai huci da yake furzarwa goshinsa sai fitar da zufa yake, ya ce “I wish I was dreaming….. bana son wannan abin ya zama gaskiya, kin fita ne da ba nan?” Ban amsa ba illa rufe idona da na yi kawai ina kokawa da numfashi na da naji yana fita ba daidai ba… Ustaz muryarsa a k’asa ya furta “Stop it Aysha! Na yi alk’awarin ko duka dukiya ta zata k’are sai na wankeki daga wannan laifin…. Zan kuma tsaurara bincike har sai na hango waye ya Miki wannan sharrin…” Da sauri na girgiza Kai na ce “Ba na so Ahmad, ka bari kawai su min duk abinda ya dace, ba Wanda zai ce ba ni ba ce a jikin hoton nan don haka wahalar da kanka kawai zaka yi…” Kuka na saki sosai, kukan da tuntuni nake son yinsa bai zo ba sai yanzu… na dinga kukan har Ahmad ya jani jikinsa bai damu da dau’dar da take jikina ba ya manna min Hot kiss Wanda hakan yasa naji zafin zazzab’in da jikinsa ya d’auka… Da k’yar ya cikani sanda aka zo aka ce lokaci ya cika. Ya harari d’an sandan sai kuma ya mik’e yana tsane hawayen da suke zuba masa a ido. Na bi bayansa da kallo hawayen na cigaba da yi min suntiri a idona. K’irjina ya min nauyi sosai kamar an saka min block ten inches a kaina. ZAMAN KOTU (COURT)…. Kaina a k’asa yake saboda na kasa yarda na ha’da ido da dandazon jama’ar da suke zube a court d’in. Hannayena duk a gark’ame da handcuffs. Lawyoyi ne birjik a gaban court d’in sai a sannan nake jin ma mutumin da aka kusa kashewar aka kwashe musu American dollars wai Minister ne. Shigowar Alk’ali ne yasa court d’in ta samu bak’uncin shiru.. hakan yasa na d’an d’ago kaina na saci kallon jama’ar da suke court d’in. A gaba na hango kaf yayyena sai Ustaz da yake saye cikin jallabiya idanunsa da black shades fuskarsa ba walwala ko ka’dan. Na d’auke idona a Kansa ina Jin zuciyata na sake k’arfafa min tsanar aurensa ba don komai ba ina tunanin silar Auren nasa muka rasa duk wani farin ciki a gidanmu. Ba mamaki da ban ha’du da shi ba duk wa’dannan ibtila’in ba zasu same ni ba. Al’kalin na kalla sai Naga na San shi mutumin Abba na ne sosai don Abbana ma Alk’ali ne kafin ta ajiye aikin da kansa… Alk’ali ya gabatar da kansa kafin lawyoyin mai k’ara da na wa’danda ake k’ara suma su mik’e su gabatar da kawunansu. Barrister Jamilu Nashe… shine lawyern da zai kare ni… Sunana suka tambaya na kuma sanar musu sannan Barrister Fateemah J. Nashe mai kare mai k’ara ta matso don yin tata tambayar. Duk tambayar da ta min kasa bata amsa ko guda na yi saboda yarda zuciyata ta yi wani irin nauyi ga idon mutane a kaina. Har sai da ta sake maimaita tambayar “Ayshatu me ye ha’din ki da Minister D’an Audu da har kika yi k’ok’arin kashe shi bayan kun k’wace masa dukiya mai tarin yawa…” Na girgiza kaina murya a shak’e na ce “Ba ni ba ce.” Ta ce “Ba ke ba ce kamar Yaya? Bayan ga zahiri an ga kamanninki kwabo da kwabo a hoto? Kuma da bakin ki kika amsa a station cewa ke ce?” Runtse idona kawai na yi ina fisgar leb’ena hawaye suka fara zubo min na k’i kuma na ce komai naja bakina na tsuke.Barrister Fateema ta jijjiga Kai ta ce “Ya mai girma mai shari’a da alama Aysha ta shirya wasa da hankalin kotu, bayan hoto da komai Sun nuna ita ta aikata abinda ake tuhumarta da wannan damar nake rok’on kotu da ta zartar da hukuncin da ya dace da Aysha ba don komai ba sai don Jan hankali ga b’aragurbi irinsu Aysha…” Da sauri Barriste Jameel ya mik’e ya ce “Ya mai girma mai shari’a bai kamata kotu ta yi hukuncin gaggawa Akan wannan baiwar Allahn ba alhali ba a tabbatar da laifin da ta aikata ba, tsananin b’acin rai yakan saka mutum ya amsa laifin da ba nasa ba. Hoto kuma ba zai zama hujjar da zia saka a kamata a nanik’a mata k Laifin da ba nata ba, duba da cewa za’a iya kwaikwayar fuskar mutum don son jingina masa wani laifi da bai aikata ba. A bada dama ta hanyar tsaurara bincike a kuma gano sauran y’an uwanta idan suka zo suka tabbatar itace sai a zartar mata da hukunci da ya dace. Dafatan Kotu zata amince da wannan nazari nawa…” Alk’ali ya jinjina Kai kafin ya yi rubutu ya d’ago ya ce “Bisa ga tarin hujjojin da Barriste Jameel ya bayar kotu ta gamsu ta kuma d’age saurarar k’ara zuwa zuwa ashirin da bakwai ga watan nan da muke ciki, kafin nan kotu bata amince da bada belin Wanda ake tuhuma ba…” ya buga guduma daga nan shari’ar ranar ta tashi. Ina kallo aka sake ingiza k’eyata zuwa motar shiga ba biya. Na dinga kallon su Ustaz da suke share hawaye akai akai. Haka aka sake gark’ame ni a d’akin da zan kira k’anin kabari, dalili ba wuta ba haske ba fanka a ciki. Window k’walli guda ne kuma d’an mitsitsi a can saman katanga. Zuciyata ta yi rauni na zube a wajen ina sakin kuka a hankali. Daga ranar ban sake saka kowa a idona ba, sai lawyer na Ustaz Jameel da yazo ya min tambayoyi Amma amsa guda bake bashi ni ban sani ba…. Ranar zaman kotu na biyu suka sake zuwa suka tafi da ni. Wannan karan ma Kotun a cike take mak’il da jama’a. Ban yarda na bu’de idona ba saboda hasken sai Naga ya min yawa. Ko don na da’de ban ga hasken ba ne. Na dubi inda jama’a suke. Anan na hango Duka y’an gidanmu. Sai Ustaz da yake gefe ya sunkuyar da kansa yana murza goshinsa. Na mayar da duba na wajen lawyoyin da suka mik’e suka fara gabatar da kansu. Mami na furta a hankali ganinta sanye da rigar lawyoyi fuskarta ba fara’a ko ka’dan idanunta sanye da black shade… sai a sannan na tuna Mami fa lawyer ce mai zaman kanta. To me tazo yi? Wa kuma tazo karewa? Ban amince a fitar min da pages d’in da ban Saki a normal groups ba. Jdan kin San kin siya Vip be don ki fitar Uwar gwaninga gaya min da wuri na baki ku’dinki. Ko ban ce ban yafe ba na san Allah ba zai k’yaleki ba dalili? Na bayar da kyautar ina kan bayarwar ma. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA …..44. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Shiru na mata, don ba amsar da zan bata, na shige toilet na ‘daura alwala. Ina fitowa na sake ganin still ta koma barcin murmushi kawai na saki ina tunanin abinda Ustaz ya aikata. Sau biyu yana shigowa d’akin da daddare yana min inkiya da na tashi mu tafi, turo baki na nake fuskata a tsuke na girgiza masa kai. Sai ya karyar da kai kamar yaro yana neman Uwarsa. Yana kallon Inna da take barci ya ce “Ki tashi mu tafi, tunda Har ta yi sallah ta sake komawa barci ba zata tashi ba, wallahi na yi alk’awarin ba abinda zan miki, sai d’an Kiss kin san bana gajiya da bakinki ban k’i kullum na dawwama a haka ba.” Harara na watsa masa na tab’e bakina na ce wallahi ba inda zani, kuma don ka ji ma Har yau ina nan kam baka na ka sakeni kafin ka wuce da matar so…” wani kallo ya jefa min yana sakin murmushi k’asa k’asa ya ce “Matar so? Mhmn, ai ni bani da matar son da da wuce ki, ki tashi mu je ko sai na d’auke ki.” Wannan karan tsuke fuskata na yi sosai na mayar da kaina na kwanta don haushinsa nake ji sosai. Ina kallo ya hawo gadon ya jani jikinsa “Shikkenan, tunda ba zaki tashi ki taya ni ha’da kaya ba, bari na kwanta anan…” na bu’de ido ina kallonsa a hankali na ce “Wallahi ka tashi ba ruwana idan Inna ta farka fa? Na San dole zata farka…” Ya sumbaci bakina yana furta “To menene don ta farka? Tun kafin a haifo iyayenmu ta San me ake aikatawa a cikin aure.” Ya fa’da yana k’ok’arin zuge min zip, na yi saurin rik’e hannunsa na ce “Tashi kawai mu tafi, Amma wallahi kada ka sake ka tab’a ni, don ban shirya zaman aure da kai ba…” sauka ya yi ya bi bayana yana dariya muna fita corridor na ji ya d’aga ni cak muka haye sama. Wani irin dare ne da sam ba zan manta da shi ba, duk da bai k’etare dokar likita ba Amma na ji a jikina na kuma tabbatar Ustaz yana bala’in sona a yau kam, shi yasa naji zuciyata tana rauni akan ramuwar gayyar da nake son na masa… sai da muka yi wanka sannan na mik’e ina niyyar fita ya sake ja na jikinsa a hankali ya zaunar da ni samar cinyarsa a kunne ya ce “K’alb, ki ce kin yafe min, please! Bana son tafiya na barki kina Fushi da ni, 3weeks kawai zan yi na dawo sai mu koma da ke, tunda aiki e da zai d’auke ni tsawon 3months, hope kin hak’ura?” Na girgiza kai na idona na kawo k’walla na cije leb’ena na ce “Ta yaya kake zaton zan hak’ura? Kana son ka ce min na hak’ura da duk abubuwan da ka min, Har da munanan maganganun da ka dinga jifa na da su, Karuwa fa Ustaz karuwa ka dinga ce min, kai da y’a kamata ka zama kai ne farkon mutumin da zaka shaideni, ba zan b’oye maka a yanzu kam bana jin sonka ko ka’dan, gaba d’aya ya fice min a rai kawai dai zan zauna da kai ne zuwa wani d’an lokaci bana son a karo na biyu a sake jin aurena ya mutu, na San zan shafawa kaina bak’in paint ne, amma da gaske bana son aurenka a yanzu kam….” Kuka ne ya k’wace min na zame daga jikinsa na mik’e da sauri duk da kiran da yake min ban saurare shi ba na yi hanyar fita, ban tsaya ko ina ba sai cikin d’akina na kuma mayar na kulle har da murza key na bar mukullin a jiki. Na jingina da k’ofar wani kuka mai saka k’unar zuciya y’a cigaba da zuwa min. Haka na kife a saman gado na dinga kukan ba k’akkautawa. Da Asuba Inna ce ta tashe ni sallah, bayan na idar da sallah na ji wata matsananciyar yunwa hakan yasa na tafi kitchen ba shiri daidai lokacin Ustaz ya fito tsaf cikin shigar Black suit da Riga long sleeve a ciki Ash color. Ba k’aramin kyau ya yi ba Amma hakan bai saka na saki fuskata da na tattara na tsuke ba na shige kitchen da sauri, ina shirin kulle k’ofar ya saka hannunsa banda tausayin musulunci ba abinda zai hana ni datse hannunsa, wato tafiyar zai yi ya bar ni da y’ar gold d’in tasa, zai tafi honeymoon ya tokare k’ofar yana k’ok’arin lallai sai mun ha’da ido ni kuwa na b’ata fuska ina d’auke kai na na juya baya na koma kitchen d’in. A gaban fridge na tsaya ina duba abinda zan iya ci. Ban yi auneba na ji shi a bayana ya min kyakykyawar runguma yana sakin ajiyar zuciya. A kunne ya rad’a min “Haba K’alb ki tsaya mu yi sallama mai kyau mana, kina kallo tun d’azu ake kirana zan iya missing flight fa…” “d’aure maka k’afafu na yi?” Na fa’da ina janye jiki na. Ya yi narai narai da idonsa da suka tara k’walla ya furta “Ba kyau fa, mala’iku zasu… ki daina yiwa Mijinki tsiwa…” Hancina na gatsine na cigaba da abinda nake. Still ya sake rungumata yana bani wani irin hot romance da suka kusa zautar da ni. A hankali ya janye jikinsa yana mayar da numfashi ido a lumshe ya furta “Allah na gani wannan tafiyar a dole zan tafi na barki, banda Mommy ma ta kafe ni zan iya hak’ura da duk abinda zan samu a wajen aikin…” na tab’e bakina kawai haushi kamar ya kasheni zai wani fake da Mommy Ai dama can ya shirya tafiyarsa yanzu ne zai canja mind d’insa da ya kusance ni ya ji ni dal, ai kuwa zai sha mamaki. “Na bada sak’o anjima za’a kawo Miki, sannan Aliyu zai zo ya dinga koya Miki mota…” “Bana buk’ata.” Na furta ina jan jikina na fice daga kitchen d’in. Ina ji ya saki ajiyar zuciya. Ina zama a gefen gadon ya shigo bedroom d’in jikinsa a sanyaye ya durk’usa har k’asa ya gaida Inna da sanar da ita zai yi tafiya. Inna ta masa fatan alheri sannan ya mik’e sai kallona yake na San so yake mu ha’da ido ni kuwa na fuske. Yana fita Inna taja tsaki ta ce “Yau Naga shegantakar banza, zai yi wannan k’ololuwar tafiyar amma ba zaki raka shi mota ki masa a dawo lafiya ba? Idan wata matar arziki ce ba har tashar jirgin zata raka shi ba. Maza ki mik’e kafin na sab’a miki.” Haushi kamar ya kashe ni haka na fice daga d’akin ko hula babu a kaina. A kujera na ganshi zaune a parlorn ya rik’e kansa. Na tsaya daga gefensa fuskata a d’aure hannu ya saka ya jani jikinsa kafin na ce komai ya manna bakinsa cikin nawa. Tsawon minti biyu kafin ya sake ni ya manna min atm card a hannu na yana furta 5656.. Ya mik’e da sauri ya fice daga gidan. Lumshe idona na yi wasu hawaye da ban san kona menene ba suka zubo min. Ina jin tashin mota fargabata da haushinsa Har ma da mommynsa da matarsa suka k’ara k’ulle ni.hawayen na share sannan na mik’e jiki a salub’e na koma d’aki. Ina ji Inna na magana ban amsata ba na shige cikin bargo hancina sai shak’ar k’amshin turaren Ustaz suke musamman Atm card d’in da ya bani, na lumshe ido na kawai. Wayarsa da ya bar min ta fara k’ara ina dubawa naga sak’o ta turo min. “Na tafi na bar zuciyata a hannunki, duk da ke ce zuciyar tawa… I missed you K’alb, I missed your cutable lips… I missed…. Sai ya saka emojin murmushi ya furta “Kunyarki nake ji ba zan iya fa’dar sunansu ba Amma dai ki kula min da twins d’ina da suke k’irjinki… I love them kana dawo naga komai ya same su…” K’irjina kawai naji ya buga da kalamansa na cillar da wayar gefe a raina na ce yanzu haka itama yana can yana mata da’din baki mayaudari kawai… Around twelve sai ga Khadija k’anwarsa ta shigo gidan. Da murmushi na tareta itama ta mayar min da murmushin ta rungumeni kafin ta isa gaban Inna ta durk’usa ta gaisheta. Inna ta mik’e ta fita parlor. Khadija na kallona ta furta “Anty Eehsha, in bi ta bakin Mijinki ya ce lallai sai na dinga ce Miki Anty wai Eehsha, gaskiya kin sake kyau abin ki dole Yaya Ahmad ya dinga rikicewa meye sirrin?” Na d’an yi murmushi kawai ina girgiza kai na ce “Bakomai, ya gida Ya Mommy?” Khadija ta ce “Mommy na nan k’alau, duk da gaskiya bata San nan zan zo ba, sak’on motar ki Ya Ahmad ya ce na kawo miki gata can a k’ofar gida…” dole na k’ak’alo fara’ar dole da murnata na ce “Mota kuma? Kai Masha Allah Amma na gode sosai….” Khadija ta yi murmushi ta ce “Ki godewa Allah da ya baki Mijin da yake tsananin son ki, wallahi AYSHA ban tab’a ganin soyayya irinta Ustaz ba, sanda abin can ya faru fa Har Mommy ta ce ya sake ki Wallahi baki ga tashin hankalin da ya shiga ba, ko abinci baya ci ya rame ya yi bak’i sai idanuwa. Bana manta sanda ya same ni a d’akina yana k’walla ya ce “Khadija, wallahi na san Eehsha ba zata aikata ba, Amma ya zan yi na san Mommy ba zata yarda ba ki bani shawara… wallahi AYSHA kuka na saka bana komai ba sai na tausayinku da makomar zazzafar soyayyarku. Auren Hameeda kuwa ta dole ya amince don ya tubure ba zai aureta ba sai Mommyn ta masa dabaibayi da ke, ta ce idan Har bai aureta ba to wallahi ba zata yarda ya dawo da ke ba,….” hakan da yaji y’a saka a take a lokacin ya amince amma da shara’din sai ya fara dawo da ke, gidan da yake kusa da gidanku ke ya ginawa ba don komai ba sai don Abba ya cigaba da bibiyar lamarin ki Amma Mommy ta k’i yarda ta ce Hameeda ce zata shiga tunda ta nuna tafi son gidan… nan ma hankalinsa ya tashi sai da na dinga bashi baki tukun sannan ya yarda. Kullum zancen yaya Ahmad Eehsha, Allah ya bayyana gaskiya kowa ya san ba karuwa ba ce ke…” Duk suruntun da take jinta kawai nake, ba wai don na yarda ba ni na San daga jin wannan zancen Ustaz ne ya shiryo mata shi. Ta ja hannuna tana furta “Baki yarda ba ko? Ai shikkenan wata rana zaki shaida haka, yanzu muje kiga dalleliyar kyautarki ta mallaka masa budurcinki da kika yi…” Na bita muka fita har Inna da bakinta ya kasa rufuwa sai zunduma wa Ahmad albarka take. Motace mulmulalliya mai kyan gaske naga dai tambarin marcedez a jiki daga haka ba zan iya cewa ya sunanta ba don ni ban wani taso da son mota a raina ba, ban tab’a saka ran zan wani auri mutum mai ku’di kamar Ahmad ba. Daga nan Khadija ta ce ba zata koma ciki ba gida zata koma don Mommy bata son zata zo ba. Na rakata Har vakin gate inda drivern Ahmad zai kaita gida. Ina sake waiwayen motar na shiga gida. Ina shiga Inna ta ce “Amma yaron nan ya kyauta, yanzu kuwa zan yi waya na gaywa iyayenki ai ke auren yaron nan alheri ne a gareki, gashi yana masifar son ki.” Ban wani amsata ba sai y’ar dariya da na yi na shige bedroom. Ina shiga waya na k’ara na ‘daga Naga shine ina tunanin missed calls d’insa na ashirin kenan ba kuma zan d’aga ba sai ya gaji Ya daina kiran, Har a raina da gaske nake zan rabu da Ustaz ko ba yanzu ba. Na cilla wayar cikin drawer bayan na kasheta na Zare sim d’in gaba d’aya ma. Kwana goma Inna ta yi aka yi waya maigidanta Alhaji Ba lafiya. Hakan yasa ta tattara komatsanta ta tafi gida y’a rage daga ni sai mai aikin da a ka kawo min su biyu dattijuwa da yarinya. Haka zan zauna mu yi hira da su…. Da yammacin wata rana ina zaune a parlor kaina nake tsefewa don kitson ya fara damuna Aka yi nocking. YABI na kalla na ce “Maza bu’de k’ofar…” ta mik’e ta bu’de sai na ji ta ce “Lah Anty Fat….” “Shshss…” na ji ta ce hakan yasa na juya da sauri sai naga Mami ce ta shigo tana murmushi ta ce “Ma sha Allah, ah lallai AYSHA jiki ya yi kyau.” Na gyara zama na muryata cike da rauni na ce “Mami ina yini?” Bata amsa ba sai zama ta yi daf da ni ta min side hug ta furta “Sam AYSHA Baki da kirki, ko nema na ba kya yi, rabuwar kenan? Ai shikkenan ya maki kyau, dama jikin ki nazo dubawa kuma naga da sauk’i Allah ya k’ara afuwa bari na tafi.” Ta mik’e da niyyar tafiya kallonta kawai nake jikina a sanyaye na kasa magana. Ina kallo ta nufi hanyar fita sai sannan na samu damar cewa Mami ki tsaya mana please.” Ta juyo ta min wani kallo ta girgiza kai ta fice daga gidan. Sunkuyar da kaina kawai na yi sai nake jin abinda na yi kamar ban kyauta ba. Da sauri na d’ago ina kallon Yabi na ce “Ke a ina kika San Mami?” Ta d’an yi diri-diri kafin ta ce “Ai na yi aiki a gidansu last year to da na tafi gida ban koma ba.” Na tsura mata ido kawai ina ganin kallon ne ya mata yawa sai Naga ta shige kitchen da sauri. Haka kawai sai naji zuciyata tana wani irin bugu da ban san dalilinsa ba. Kashegari again sai ga Mommyn su Ustaz. Cikin ginshira ta shigo tana min kallon ‘daid’aya da k’yar take amsa gaisuwata itama abin mamaki sai na ji ta kama sunan Asabe dattijuwar da take taya ni zama… Asaben ma a ladabce ta amsa mata. Hirar da suke ce ta bani mamaki don zahiri sun nuna sun san juna. Da zata tafi ta mik’e tana cewa Asabe mu je na ganki…” Asbaen kuwa ta bita cikin rawar jiki. A tsorace na bi Asabe da kallo har ta je ta dawo ban farka daga mamakin da nake ba. Asabe ta zauna tana dariya da sauri na kalleta na ce “Baba Asabe dama kin san Mommy?” Asabe ta d’aga min kai tana dariya ta ce “Sani kai Hajiya, ai daga can gidan aka kai ni gidanku shine aka kawo ni nan, ai nafi shekaru talatin ina yiwa Mommy aiki, banda ma baki da gane mutane zuwanki na farko ai ina gidan…” Ido kawai na zuba ina kallonta cike da mamaki. Ina kallo itama ta shige kitchen da alama taga ba zan ce komai ba ne. Haka kawai ranar sai naji na kasa samun nutsuwa ba ga Asaben ba, ba ga Yabi ba, dukkansu ba Wanda zan iya sake yarda da shi. Har na danna waya na kira Umma ganin bata d’aga ba sai na kashe wayar kawai. Na mayar da kaina na kwanta da niyyar kashegari zan kirata. Sai dai kuma wani abin al’ajabi sai na manta shaf. Har bayan kwana biyu, muna zaune a cikin gida muka dinga jin jiniyar y’an sanda. Kamar ma a cikin gidan. Haka kawai sai naji gaba na ya yanke ya fa’di. Na yi saurin jan Hasbunallah a zuciyata, daidai lokacin da aka buga k’ofar parlorn da nake da k’arfin gaske. Zuciyata ta sake bugawa Wanda ban san dalili ba. Asabe ce ta bu’de k’ofar da sauri taja baya tana dafe k’irji ta ce “Mun shiga Uku Aunty y’an sanda…” kafin na yi magana Y’an sandan matan Sun shigo suka d’aga min handcuffs a hankali suka furta “You are under arrest….” Na ware ido ina kallonsu na ce “For what?” Y’ar sandar ta min wani kallon rainin hankali ta ce idan mun je station kya ji… ta wurga min wani hoto wacece wannan idan ba ke ba? Ana zarginki da kisan wannan bawan Allahn bayan kin kwashe masa dalolinsa da kuka je hotel…..” Wata irin ka’dawa jikina da cikina suke…. Na kasa furta komai ina kallon hoton da nake sanye da bak’ak’en kaya baka ganin komai a jikina sai fuskata hannuna d’auke da bindiga a tsakiyar d’akin hotel….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA…..46. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. A hankali duka lawyoyin suka gabatar da kansu. Kafin Mammy ta mik’e ta isa gaban Alk’ali ta gabatar da kanta. Mamaki ya kama ni jin Mami zuwa ta yi don ta kare ni. A hankali lawyern mai k’ara ta isa gaba na ta tsaya tana murmushi ta ce “Ayshatu, shaidu da dama Sun bayyana cewa ke kika yi nufin kisan nan ina son kada ki wahalar da shari’a ki amsa laifinki madadin Kwan gaba Kwan baya da kike mana… ki amsa kawai sannan ki jero sunayen abokan aika aikar taki…” Shiru na yi idona a lumshe cikin wani b’acin rai na sake girgiza Kai na a karo na biyu na ce ban san su ba.” Mami ce ta mik’e tana gyara glass d’inta ta nemi izinin Alk’ali wajen yin magana ya bata dama. Har gaba na ta iso ta kalleni sosai irin kallon da take min da ina yarinya idan tana son na kwantar da hankalina… “Ki nutsu Aysha ki amsa laifin da kika San kin aikata kada ki kuskura ki amsa abinda baki aikata ba.” Sannan ta juya gaban Justice ta ce “Ba ta yarda za’a yi a ce Aysha ce ta aikata laifin da ake tuhumarta da aikatawa don kawai an ga hotonta, hoto ba zai zama hujjar kama mutum dumu dumu da aikata laifi ba. A Karon farko idan har da gaske an yi attacking minister me ya Kai ministern gayya tar su wad’anda suka yi nufin kashe shin zuwa cikin hotel d’in? Shin yana da wani deal da su ne? Me ya yi musu suka yi nufin tozarta shi? Abu na gaba akwai mutane a gidan wannan baiwar Allahn, akwai masu aiki akwai wa’danda suke kula da harabar wajen gidan ya kamata a ji ta bakinsu, shin Aysha ta fita a wannan ranar ko bata fita ba?” Alk’ali ya jinjina Kai kafin ya ce “Ina buk’atar ganin maaikatan gidan gaba d’ayansu idan zai yiwu yanzu.” Mami ta girgiza kai kafin ta ce “Na gode, ya mai girma mai shari’a suna nan a waje dama tuni na saka aka zo da su.” Ya yi umarnin a shigo da su. Sai gasu kuwa gaba d’ayansu aka jere su a gaban kotu. Mami ta dinga bin su da kallo d’aya bayan d’aya sannan ta ce “A rana ta d’aya ga watan nan da muke ciki Wanda ya kama sati uku cif fa ya wuce, shin uwar d’akin ku ta fita?” Kusan a tare suka jijjiga kai suka kuma ha’da baki wajen cewa “Ai Hajiya tun ranar da Yallab’ai ya tafi ba inda ta je gaskiya…” Mami ta jinjina kai ta ce “Ko da wannan ya isa Kotu ta yiwa 𝑨𝒚𝒔𝒉𝒂𝒕𝒐𝒖 adalci ta San cewa bata da hannu wajen kisan nan….” “Objection My lord!” Barrister mai kare Wanda ake k’ara ta mik’e “Wannan bai zai zama hujjar da za’a wanke mai laifi ba, saboda ko bakomai za’a iya ha’da baki da masu aikin gidan wajen wanketa daga zargin da ake mata, don haka Alk’ali a yi duba da wannan hoto da aka gani muraran a zartar wa da Ayshatouh hukunci ba don komai na sai don k’ok’arin kisan Kai da kuma b’atawa babban mutum irin D’an Audu suna. Ta hanyar watsa hotunan tsiraicinsa a media…” Alk’ali ya jinjina kai ya yi rubutu kafin ya d’ago yana kallon Mami ya ce ko kina da abin cewa? Mami ta sake mik’ewa ta ce “Ina da shi My lord, ina son a zo da minister nan don shima ya fa’di yarda ya ha’du da su da kuma me ya aikata musu da suka yi k’ok’arin b’ata masa suna… Abu na gaba lallai hukuma ta yi gaggawar kamo wa’dancan masu laifin don su tabbatar da 𝑨𝒚𝒔𝒉𝒂𝒕𝒐𝒖 ce ta aikata laifin idan ba haka ba kotu bata damar tsare 𝑨𝒚𝒔𝒉𝒂𝒕𝒐𝒖 bisa laifin ni da kai da kowa ma muka tabbatar ba ta aikata ba…” Alk’ali ya jinjina Kai ya yi dogon rubutu kafin ya d’ago ya ce “Kotu ta sake d’age sauraran k’ara zuwa 10 ga watan mayu kwana goma kenan cif, kafin wannan lokacin muna umartar duka b’angaren lawyoyi da su zo da shaidun gani da ido Wanda zasu tabbatar da faruwar lamarin ko akasin haka!” Wani irin fa’duwar gaba ce ta riskeni Jin yarda Kotun ta d’au hayaniya kamar me na runtse ido na kafin na Ware su ganin kamar k’amshin Ustaz ne a daf da ni. Shine kuwa yana tsaye ya Zare Shades d’in idonsa yana kallona da jirkitattun idanunsa da suka ka’da suka yi jajur hawaye mak’ale a k’asan idon. Na ji ya sunkuyo kaina. Bai yi la’akari da d’audar da ke jikina ba ya manna min Kiss a forehead a hankali ya ce “Stay Strong K’alb, In sha Allah you will be free…” na lumshe idona kawai hawaye na saukar min. Y’an gidanmu ma gaba d’aya Sun kewaye ni. Suna hawayen Umma ma na tsaye ga Abba da Inna a gefe sai rusa kuka take. Ina ji ina gani Police suka sake tasa k’eyata muka wuce. A hankali na tauna leb’e na ina Jin hucin da zuciyata take fitarwa. Har bakin motar Mami ta je tana kallona tana murmushi ta furta “Stay strong daughter, nothing will happen In sha Allah.” Sauke idona kawai na yi hawayen suna cigaba da zubo min. Ina ji aka ja motar da wata irin jiniya da ta kara’de wajen. Kashegari kuwa sai ga Ustaz ya shigo wani d’an sanda a bayansa. Ban San me ya gayawa Police d’in ba na ga dai ya juya bayansa. Ustaz ya jani jikinsa a hankali yana ha’de bakin mu waje d’aya. Bayan haka bai sake magana ba illa hoto da ya zaro min. Wasu y’an mata ne su takwas ta tsakiyarsu kam Nima na tabbatar nice cikin shigar English wears da ta fitar da duk shape d’insù. Kana ganin idanunsu ka San kunya ta yi k’aranci. A hankali Ustaz ya ce “Kin san su?” Na girgiza kaina. “Wallahi ban san su ba, ban kuma tab’a ganinsu ba.” Sai na ga ya mayar da hoton ya shiga murza goshinsa ba tare da ya sake magana ba, ya dai manna ni da jikinsa a hankali ya furta “Ya Ilahi! What happened ne?” Shiru kawai na yi a jikinsa. Shi Sam bai damu da yanayin jikina na haka ya sake manna ni da jikinsa ya lalubi bakina ya tura min chewingum d’in da yake taunawa sai Naga ya mik’e kamar ma jiri yake ya fice daga wajen cikin wani irin taku mai bayyana rauninsa. Ban iya komai ba sai lumshe nawa idon da na yi nima ina kokawa da numfashi na da sai naji kwana biyu yana sassark’e min. Ranar da za’a yi zaman kotun. Ban ita runtsawa ba saboda yarda gaba na yake fa’duwa dalili? Ban san ya shari’ar zata kaya ba. Ban san wani irin hukunci za’a yanke min ba idan aka rasa shaidar da za’a kareni. Hakan yasa na gagara komai sai salloli da na dinga jerawa ba tare da na San adadinsu ba. Hawaye kuwa ina ji da tara nake zai iya cika wani abin. Ina ji da safe aka sake shigowa aka fita dani. Wannan karan raunin da yake zuciyata ya kasa b’uya sam a tare da ni. Don tun bayan da na sauka a mota idanuna suke zubar da hawaye ga wani matsanancin ciwo da suke min Wanda na tabbatar na yawan kukan da nake ne. Jiri yana d’ibana Amma haka aka shigar da ni cikin inda zan tsaya a wajen shari’ar. Na yi k’asa da kaina bana burin ha’da ido da kowa don a jikina nake jin kamar daga yau rayuwata zata canja. Kamar daga yau iyaye y’an uwa Miji na zasu yi Allah wadarai da halayena… nan da nan aka fara gudanar da shari’ar da yau ina jin duka lawyoyin da zafin su suka zo. Dole aka shigo da mutumin da ya ce mun damfareshi mun kuma b’ata masa suna ta k’ofar baya. Ta k’asan ido nake kallonsa Wallahi ban san shi ba, ban kuma tab’a ganinsa ba ko a t.V ma balle a zahiri. Barrister Mami tana kallonsa fuskarta a tsuke ta ce “Malam, ina ka san waccan baiwar Allahn? Kuma meye ha’dinka da ita da Har suka bika hotel?” Ina kallo ya jijjiga kansa da alama lamarin yana b’ata masa rai ya ce “Sanin abinda yasa na gayyaceta hotel duk bai taso ba don zai iya zama sirrina…” “Ya kuwa taso, tunda a k’ank’antar shekarunta na sha takwas za’a iya cewa ka cuceta ka yaudareta ka saka ta abin da bai dace ba, irinku ne masu lallata tarbiyyar yara, ba mamaki ka nufi yi musu wani mugun abu ne yasa suka aikata maka wannan tozarcin don haka zamu so sanin a inda kuka ha’du da kuma yanayin mu’amalarku ta nan zamu san irin hukuncin da zamu yankewa abinda ta aikata maka idan ma ta aikata d’in.” Kowa ya kalli yanayin Mami a lokacin y’a San cike zuciyarta take da b’acin rai ta yarda lamarin ya kasa b’uya a saman fuskarta da ma idanunta gaba d’aya. Kaftawa iya kaftawa aka yi a wannan rana Amma D’an Audu ya k’i bu’de baki ya amsa laifinsa na jan yara k’anana hotel ya dai ce damfararsa dama suka shirya yi shi yasa suka aikata masa haka, yana kuma rok’on kotu ta masa adalci akan abinda aka masa. Abubuwa suka damalmale k’arshe sai da Alk’ali ya buga guduma sannan kotun ta samu bak’uncin shiru… Ya yi gyaran murya ya ce “A yau kotu zata zartar da hukuncin da take ganin ya dace, Kotu ta kama Aisha da laifin…….” “A dakata ya mai girma mai shari’a!” Aka fa’da daga bak’in k’ofa gaba d’aya idanun mutane suka koma can. Police suka shigo da wasu matasan y’an mata duka fuskokinsu a rufe aka k’araso da su, idanu suka koma kansu ni kaina kallonsu nake da son sanin su wanene? Cikin daka tsawa Police d’in ya ce “Ku bu’de fuskokinku kafin na ci Ubanku!” Suka hau yaye fuskarsu illa d’aya daga cikinsu da ta k’i bu’dewa, Har sai da Police d’in ya saka hannu ya yaye mata fuskarta idanuna suka fa’da cikin nata a tsorace a wani irin yanayi muka dinga nuna juna…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 47….. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Banda ba barci nake ba, da sai na ce mafarki na yi da mai kama da ni kwabo da kwabo. Exactly kamar ni ce a tsaye, sai dai banbancin yanayin gogewa da wayewar idonta. Don kana ganinta zaka san wayayyiya ce… na runtse ido na sake bu’dewa don na tabbatar da abinda na gani. Amma still idanuwa na suka sake sauka a kanta itama kallona take yi bata ko k’iftawa. D’an sandan da ke tsaye ne ya dawo da ni cikin hayyacina jin maganar da yake yiwa Alk’ali. “Hak’ik’a an yi kuskuren kama wannan baiwar Allahr, a aikin da wannan mai kama da itan ta aikata. Ba ita ba ce sai dai kamannin da suke da juna da akewa lak’abi da kwabo da kwabo yasa ake ganin kamar ita ta aikata. A yau Allah ya bayyana tsatsan ikonsa na kuma jinjina girma da k’udirar Allah mai yin halitta ya kuma sake maimaita irinta ba tare da kuskure ko guda ba. A yau muka yi dacen kama su a cameroun zasu hau jirgi su tafi south africa. Yallab’ai ita wannan itace Ainahin Aysha SHANY da ake nema ba wannan Ayshar ba.” Ba ni ka’dai abin ya bawa Al’ajabi ba, Har ma ya sanya zuciyata cikin ru’dani. Na lura hatta da mutanen wajen hakan ce a garesu ta yarda suka bu’de baki suna kallonmu. Ina kallon yarda Umma take Zare ido kamar yarda Mammy da Abba ma suka shiga shock. Ita kuwa Aysha sai nuna ni take da yatsa sai dai ta kasa furta komai. Fuskarta ce dai d’auke da tsananin mamakin da ya kasa b’uya a idonta. Sai k’ikkifta kyawawan idonta take. Mai shari’a dai tsabar ru’dani ajiye biron ya yi, yana jijjiga kansa ya ce “Hukumullahi laaa ajaban.. wannan lamari to ya abin yake ne?” Bayan tsawon mintoci da samun hayaniya a parlorn. Alk’ali ya mayar da glass d’insa ya kuma dakatar da hayaniyar ta hanyar amfani da guduma ya buga table d’in da ke gabansa… nan take kowa ya nutsu aka kuma kasa kunne don cigaba da sauraran shari’ar. Kowa ba son jin yanke hukunci yake ba, so yake yaji ya aka yi aka samu wannan matsananciyar kamar da muke da juna. A idanunsu na gano hakan. Ni dai ina tsaye sai mayar da ajiyar zuciya nake ina sake ware idona ina kallon SHANY da take tsaye tana ta fisgar leb’enta da alama yanayin ya zame mata jiki. Idanunta kuwa kamar ma a buge take tsabar yarda suke lumshewa da kansu. Maganar da Alk’ali ya yi ne yasa na d’auke hankalina a kanta na gyara tsayuwata ina sauraran abinda ya ce. “Baiwar Allah ko bayin Allah, da gaske ne ku kuka yiwa Minuster D’an Audu sata bayan kun same shi a hotel kun shak’a masa abin Maye kuka yi amfani da wannan damar ku ka d’au hotonsa kuka ya’da a social media kuna nuna tsiraicinsa… ko da yake kafin nan zan so sanin sunayenku da na iyayenku garin da kuka fito da komai ma ina son sani…” Ya fa’da yana duban su. Gaba d’aya suka shiga kallon juna d’aya bayan d’ayansu suka shiga nuna mai kama da ni. Da alama itace shugabarsu ita kuma zata wakilcesu. Ba tare da shakkar komai ba ta gyara tsayuwarta tana cigaba da juya idonta exactly irin na y’an Maye ta ce “Sunana SHANY, haka na taso na ji ana kira na a gidan da na rayu. Na ji ana kirana da SHANY. Aisha shine cikakken sunana. Sunan Uba ko wakili kuwa ba ni da ko d’aya, ban kuma San su ba….” Gaba d’aya naga y’an gidanmu Sun zaro ido. Musamman Umma da Abba. Mami kuwa k’asa Naga ta yi da kanta. Shi kuwa Ustaz Ware idonsa ya yi sosai sai ya kalleni sai ya kalleta. A raina na dinga nanata sunanta wato itace wacce aka zata ni ce a jikin wancan hoton na farko Har Ustaz y’a sake ni saboda shi… Cikin fuskar mamaki Alk’ali y’a zuba mata ido kafin ya furta ban gane baki san iyayenki ba? Shi mahaifin naki mutuwa ya yi ko kuwa sallmaki ya yi kika shiga rayuwar bariki?” Muryar ta a shak’e ta furzar da huci ta ce “Na ce maka ban san su ba. Hakan yana nuni da amsar kai tsaye bani da su.” Alk’ali ya girgiza kai ya ce “Mahaifiya fa?” Sai naga ta saki malalacin murmushi tana juya kai ta furta “Babu! Ni y’ar tsintuwa ce, kamar yarda wad’annan da kake gani suma duk y’an tsintuwar ne, kai gaba d’aya k’ungiyarmu ma y’an tsintuwar ne mun tashi a k’ark’ashin kulawar wata mata…” Ido kawai naga an zuba mata nima Kallonta nake cikin matsanancin mamaki. Alk’ali ya ce “Ikon Allah! Ita matar kuma bata San iyayenku ba take rainonku?” Ina kallo SHANY ta d’an yamutsa baki kafin ta girgiza kai da alama ta gaji da question d’in Alk’alin. “Shegu ne mu, haka uwar gijiyar mu Atine harka take gaya mana bamu da wasu dangi bayan ita, ita ta rainemu ta kula da mu har muka kawo yanzu bayan iyayenmu Sun cillar da mu….” Alk’ali ya yi rubutunsa kafin ya d’ago ya zuba mata ido ya ce “Ina son sanin tarihinki…” Ta sake turo bakinta cikin yanayin tsiwa ta ce “Atine y’ar harka shine sunan wacce take kula da mu tun da muka tashi ita muke gani ita kuma muka sani. Tun muna yara tare muka taso da wa’dannan, su na sani a matsayin y’an uwana. Sune dama sa’annina a gidan Babu wani mai cikkaken asali a cikin Mu. Takurawar da Uwar rik’onmu take mana yasa muka tashi da k’untutaccuyar zuciya mai zafin gaske da k’unci. Wahalar da mu take tamkar bayi. K’alilan daga cikinmu take warewa ta saka a makarantar boko Wanda kyansu ya kai kyau, hakan yasa ta saka ni a makarantar nima don ta sha fa’da ni jarinta ce, kuma wacce ta bata amanar kula da ni a kullum tana jik’ata da naira. Na yi makarantar private school tun daga nursery Har Secondary school, yanzu ma Ina jami’a. Tana bani abinci mai kyau sutura mai kyau ba don komai ba sai don na yaudari k’usoshin gwamnati hakan yasa bata gajiya da siya mana sutturu masu alfarma da supplement na gyaran jiki. Yaudarar maza muke ta hanyar nuna shigar banza don tun yarinya tana shekaru sha hu’du dama zata fara koya mata duk wata hanya da ta San zata mallaki namiji da dukiyarsa. A duk inda masu ku’di suke muna zuwa mu zak’ulosu mu kuma yaudaresu bayan sun saki jiki da mu sai mu saka musu abin Maye a abin sha mu yashe dukiyarsu mu d’auki hoton tsiraicinsu mu ce da zarar sun fa’da sai mun ya’da a social media. Har zuwa yanzu da muka yaudari Minister d’an Audu!” Daga haka ta ja d’an mitsilin bakinta ta tsuke tana cigaba da ka’da jikinta. Da alama sam ba abinda yake damunta balle ta shiga cikin fargaba sai far far take da idonta da ya sha eyeliner. Alk’ali ya jinjina kai yana sake kallonta ya ce “Yanzu ina uwar d’akin taku take?” D’an rausayar da kanta ta yi kafin ta furta ta ce “Tana Abuja ta ce kada ma mu nuna min santa mu je mu yi ta kanmu, wannan ne dalilin da yasa na d’au alwashin sai na tona mata asiri… ta ce d’an Audu bai da mutunci da dai wani ne tana da hanyar fito da mu.” Alk’ali ya sake jinjina kai ya ce “Ikon Allah! To ina kuke kai ku’dad’en da kuke yin fashi? Ko damfara zan ce?” Alk’ali ya jinjina kai ya ce “Ku bada address d’in inda za’a sameta. Kafin nan zaku zauna a hannun hukuma Har zuwa lokacin da zata zo mu tabbatar da abinda kuka gaya mana gaskiya ne…. Da wannan nake cewa Kotu ta wanke Aisha daga zargin da ake mata… muna kuma rok’on ta yiwa jama’a afuwa akan kuskuren da aka samu… Za’a dawo shar’ai sha bakwai ga watan nan da muke ciki… daga haka ya buga gudumar kotu d’aukacin jama’ar da suke wajen suka furta “Kotuuuuuuu!” Wanda ya yi daidai da isowar duka zuri’ar gidanmu wajen har Ustaz da bakinsa ya kasa rufuwa. Na dinga kallonsu da wani irin yanayi da ni kaina na kasa tabbatar da abinda nake ji. Haushinsu da haushin rashin yarda da ni da suka yi ya nanna’de duk farin ciki na. Na dinga jin wani irin zafi a zuciyata. Idona ya sauka kan Mami da take zaune kanta a k’asa na lura tun d’azun bayan bayyanar SHANY a yanayin da take ciki kenan….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….49. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Yaya Usman yana dariya ya bar wajen. Ni kuwa harara na bi bayansa da ita ina kiciniyar k’wace kaina da ga wajen Ustaz da ya manna ni da jikinsa kamar zai mayar da mu Abu guda. Idanunsa a lumshe suke sosai yana k’ok’arin aika sak’on da yake so ya aika ta hanyar manna min zazzafan kiss da na ji shi har tsakiyar kwanya ta. Cikin kunnena ya min magana. “Ki shiga ki musu sallama mu tafi gida K’alb, jikina na wani irin missing d’inki.” Na yi k’arfin halin tureshi daga jikina ina sakin tsaki na ce “Wallahi ba zan koma gidanka ba Ustaz ko me zai faru sai dai ya faru….” Murmushi ya saki ya ce “Ko? Ki ce Ashe Abba zai shirya samar mana d’aki a nan shikkenan Nima sai na dawo nan, kin ga ko aiki ba zaki dinga yi ba sai dai mu wuni muna raya sunna…” na zuba masa harara na ce “Ka d’auka wasa nake? To bari ka ji na maka ta yara billahillazee na gama aurenka… Allah ya kiyaye na zauna da mai mata, ka je can ka jagwalgwalata Nima kazo ka jagwalgwalani na bar maka Hameeda Amma ni wallahi a yanzu dai kam saurayi gal nake so…” Shiru ya yi yana kallo na. Kafin Naga idonsa ya ka’da ya yi jajur ya janyo ni jikinsa muka tsaya daf da juna da sauri na runtse idona don ba zan juri ha’da ido da shi ba, don idon nasa a rikice suke. Cikin dasashshiyar murya ya ce “Open your Eyes and look at me… ki fa’da min ba kya so na Mara kunya…” Ya fa’da yana zagaye fuskata da yatsun hannunsa “Oya talk mana, madam parrot.” Da sauri na runtse idona jin yarda ya zura harshensa a kunnena bayan ya saka hannunsa cikin rigata. Na ji ya saki wata ajiyar zuciya da ta saka ni Jin kamar na saki fitsari. Tsawon lokaci ina jikinsa na kasa Zare jikin nawa sai can na ji ya sake ni ya kwanta flat a saman gado idonsa a lumshe.. “Ke da kanki kin yi missing d’ina amma kafiya da taurin kai sun hana ki ki gane, sai yaushe zaki daina wahalar min da zuciya ne?” Ya fa’da yana zagaye ni da kasalallen idon sa da suka jirkita zuwa wani launi da duk Wanda ya ganshi zai gane. Na mik’e tsaye cike da tsiwa da masifa na ce “Sai sanda ka sakeni. Malam idan sonka zai kasheni sai fa ka sake ni, idan ma ina son naka kenan.” Daga haka na juya da sauri na fice daga d’akin haushina guda yanda k’amshin mayataccen turarensa ya mak’ale a kaya na. Gashi ba dama na canja Kayan da Zarar na canja kowa zai yiwa abin mummunar fahimta. Tilas na zauna da Kayan da duk inda na motsa sai naji k’amshin turaren da yake jefe ni a wani yanayi. Ina son Ustaz son da ya sabbaba min zafin kishinsa nake jin Sam ba zan iya ha’da shi da wata ba. Ga zafin mahaifiyarsa da nake ji a raina don haka dole zan hak’ura na bar mata d’anta. Da daddare….. Kamar kowane lokaci da aka Saba a lokutan baya UMMA ta shirya abinci. Abin haushi sai ga Ustaz ya zo don Naci a Daren ma. Kyan da ya yi yau har ya zarce misali. Sam bai ji kunya ba ya zauna a cikinmu duk inda na yi kuma idanunsa suna zube a kaina. Cin abincin ake ba mai magana sai dai ni da Ustaz da y’a taku rawa na lura shima ba abincin yake ci ba. Sai da aka gama sannan Abba ya yi godiya ga Allah ya yi addu’a mai tsawo sannan ya dubi UMMA ya ce “Ina tsammanin wani al’amari game da yarinyar nan mai kama da Aysha. Ina hasashen ko daga tsatsanmu take musamman masu kamar A’isha a dangin nan suna da yawa kasancewar da Mahaifiyar Alhaji suke kama don haka na ce lawyoyi su tsaurara bincike har sai an gano marik’iyarta da yarda aka yi ta tsinceta saboda kamannin Sun yi yawa. Banda a gaba na aka fito da ita lokacin da kika haifeta tabbas da na ce y’an biyu kika haifa.” Umma ta ja ajiyar zuciya ta ce “Ashe ba ni ka’dai abin nan ya tsayawa a rai ba, kamaninn ga sun b’aci kamar irin y’an biyun nan da ake kira Identical twins fa Wanda ba’a gane su sai da shaida. Amma kuma ai ba Wanda ya tab’a rasa y’arsa a dangin nan… Abba ya ja ajiyar numfashi ya ce “Gaskiya, ba Wanda ya tab’a rasa y’arsa a kaf danginmu daga na nan jihar har ba potiskum, Amma ina Jin lamarin yarinyar nan a zuciyata kamar jini na, kuma na tausaya mata da ita da y’an uwanta da aka raina cikin irin wannan bak’ar rayuwar, koda an bincike ba a dangi take ba, ni zan d’auketa da sauran y’an uwan nata da ba’a samu danginsu ba In sha Allah.” Umma ta ce “Gaskiya hakan ya kamata ka yi, Ubangiji Allah ya tayaka rik’o, Allah yasa ma tana d’aya daga cikin ahalin wannan zuri’a tamu.” Sam zancen su bai wani burgeni ba a zuciyata haushi ma na ji saboda me za’a d’au mutanen da suka yi silar afkawa ta cikin bala’i? Na dai bi su da ido kawai. A ranar kam k’emadagas na k’i na je wajen Ustaz duk da lallab’a ni da suka dinga yi na yi burus da su na shige d’aki, Abba ya ce a k’yale ni na huta. KASHGARI….. Tun da na tashi da safe, na ji zuciyata ba abinda take so irin na ga Mami na. Hakan yasa na shirya tsaf cikin wata tsadaddiyar Abaya ta peach color mai masifar kyau. Ina fita parlor na zube a gaban UMMA ina rok’onta ta bar ni na je na ga Mami na. Shiru Umman ta yi kafin ta ja ajiyar zuciya ta ce “Ayshatu y’ar gidan Mami, ni ba zan hana ki zuwa ganin Maminki ba Amma na San ko kin je ma bai zama lallai ta saurareki ba.” Na marairaice fuska ina cewa “Ni dai UMMA ki bar ni na je.” Ta d’aga Kai “Ki je Aysha Amma kada ki da’de tun da mutane suna zuwa Miki murna.” Har na mik’e na ji UMMA ta tsayar da ni ta ce “Au, tsaya Aysha kin tambayi Ahmad ne ai ya zama dole ki gaya masa kafin ki fita, tunda da igiyar aurenki a Kansa.” Gaba d’aya na b’ata fuska ta na ce “Umma wane irin na tambayeshi kuma? Ni fa wallahi UMMA ba zan koma gidansa ba, don har yanzu ban manta abinda ya min ba, k’arshe shine har da aure ban sani ba, ni wallahi bana son zama da kishiya na je ina wani raba miji da ita…” Baki Umma ta saki tana kallo na kafin ta ce “Cab’di, ba shakka, kanki d’aya kuwa Aysha? Ba zaki raba miji da wata ba, to kin ci gidanku shin mu nawa kika bu’di ido kika gani a wajen Uban ki? Gwara ma ki sahhalaewa kanki tunda kika zo A Nigeria dama a wata k’asar ne sai na ce mafarkin ki zai zama zahiri… shin menene ma laifin Ahmad da zaki ce ba zaki koma gidansa ba?” Rau rau na yi da idona na ce “Umma baki ji fa irin maganganun da yake gaya min ba, duk Akan laifin da ba nawa ba, sai da yaga ba haka bane sannan yake son kare kansa, ga mahaifiyarsa ba irin tsanar da bata nuna min ba. Allah ya kiyaye na koma wani gidan Ustaz…” Umma kallona kawai take cikin matsanancin mamaki ta ce “Duk na ji, ai mu ma iyayenki mun miki laifin me yasa kika yafe mana?” Na girgiza Kai na ina fincikar leb’ena na ce “Ku daban, shi daban, bari na yi sauri na tafi.” Ban jira UMMA ba na fice da sauri ko driver ban tsaya jira ba na tafi Titi da kaina Neman adaidaita sahu. Tunda na shiga gidan Mama take jifana da kallon banza, ko amsa gaisuwata ba tayi ba, ta hau ni da fa’da cikin b’acin rai. “Aysha Fateema ba uwarki ba ce, ku barta ta huta tunda gaskiya ta riga ta bayyana bana son na sake ganin sillan k’afafunki a cikin gidan nan kin ji na gaya Miki.” Turo mata baki na yi na ce “Da’dinta ba wajenki na zo ba, wajen Uwata na zo, kuma wallahi sai na ganta babu Wanda kuma y’a isa ya ce Mami ba uwata ba ce, don haka ki bar wani balok’ok’o kafin ki tada hawan jininki a banza…” na haye sama ina dariya ganin yarda ta zaburo a guje. Sai da na tabbatar na kai inda ba zata iya Cafka ta ba sannan na juya na mata gwalo na ce “Ki biyo ni mana, idan kina da k’afa gurguwar tsohuwa kawai.” Ina ji ta ce “Ba shakka! Za ki sakko ki same ni ne.” A hankali na tura k’ofar d’akin Mami na. Wannan karan a zaune na sameta tsaf da ita cikin kwalliya sosai sai zabga k’amshi take…. Ta d’ago tana kallo na da mamaki ta ce “A’isha ke ce da safen nan? Ho ho ho! Aysha Sam ba kya girma, idan banda haka daga fitowarki jiya shine kika zabaro k’afa kika fito.” Zama na yi a jikinta na rungumeta sosai na ce “Mami na ina missing d’inki shi yasa wallahi gidan ba da’di shi yasa, don Allah ki koma gidan mu Mami…” wani irin kallo ta hurgeni da shi kafin ta jijjiga kai ta ce “Ni da gidanku Aysha har abada! Babu sunan da nake kiran gidanku a yanzu haka sai BAKIN GIDA…. Idan ma abinda ya kawo ki kenan gwara ki tashi ki tafi.” Idona ya cika da k’walla ganin yarda b’acin ran Mami ya bayyana ainun.. na gyara zama na a jikinta ina sakin kuka. A hankali ta saka hannunta tana bubbuga baya na ta ce “Ki yi shiru ba abinda zai raba ni da ke. Am still your caring mother… ya labarin wannan yarinyar kin ji ana zancenta a gidanku?” Sam na manta wace yarinya ce don haka na ce mata “Wacce Mami?” Ta d’an cije leb’enta ta ce “Your carbon copy, me kika ji Imamu ya ce a kanta ko shi ko Ummanki?” Na gyara zama na ina kallonta na ce “Me yasa kike son sani?” Ta girgiza kanta ta ce “Komai ma, kawai gaya min…. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢✍️★ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA…..48. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Na yi saurin zame hannuna da Naga Ya Usman da ya rik’e ni. Na isa wajen Mami a hankali na fa’da jikinta ina sakin kuka na furta “Mami na!” Tsam na ga ta yi tana kallona da hawayen da suka jik’a mata idanu, sai naga ta janye ni daga jikinta da sauri ta mik’a a hanzarce ta bar wajen. Jikina a sanyaye na bi bayanta da kallo. Anty Khadija ce ta zo ta kama ni tana furta “Tashi AYSHA mu je gida ki huta.” Na kalleta da idona da suke zubar da k’walla sai ta girgiza min kai ta saka hannu tana share min k’wallar a hankali ta furta “Yau ranar farin ciki ce AYSHA ba ranar kuka ba.” Ban fasa kukan ba don ji nayi kamar yanzu abubuwan suka dinga faruwa. Na bi bayanta ina kallon yarda kowa na gidan mu yake yi min kamar ya lashe ni. Na tuna wa’dancan idanun nasu na wancan lokacin da suka dinga yin kamar su kashe ni don haushi. Fuskata na tsuke musamman hango Ustaz da na yi fararen hak’oransa Sun k’i su rufu, haka kawai sai naji haushinsa y’a tokare min a k’irji. Ido na zubawa Umma na da take ta kuka kamar me? Na d’auke kaina kawai bayan na yi k’asa da idona ina wasa yatsun hannuna. Dukkansu haushinsu nake ji kamar yarda zuciyata ta kasa musu uziri. Ya Usman kawai na rab’u da jikinsa ya dinga buga min baya a hankali yana furta “Am happy for your happiness AYSHA.” Ya ja hannuna yana furta “Ya kamata mu tafi gida haka, ki je ki huta ki samu isashshen barci.” Hakan yasa duk Naga sun biyo ni. Ustaz ma yana gefe na kamar ya janye ni daga jikin Yaya Usman ganin yarda yake ta shiga jikina. Muna fita y’an jarida suka mana caaaa ni kuwa na runtse ido na haushi da takaici kamar ya kashe ni duk tambayar da suka min kawai sai na saka kuka na ce Alhamdulillah!” K’arshe dai na ji Ustaz ya janyeni da sauri na koma gefensa direct inda motocinmu suke ya nufa. Ganin yarda kowa yake k’ok’ari sai na bi shi hakan yasa Abba ya ce “A’a ta bi Mijinta, idan ta huta sai ya kawota gida.” Zuciyata ta yi wani irin zillo a raina na ce “Ai kuwa wannan karan zaku sha mamaki, ba zan koma gidan mutumin da Uwarsa bata so na ba.” Don haka na ja hannun Ya Usman na fa’da motarsa ina cewa “Kai ni gida Yaya Usman, kaina kamar zai tsage.” Ba Wanda ya lura da shigata motar don ina ganin suna ta waige waige. Ya Usman kuwa ko matarsa bai nema ba ya ja motar da k’arfi muka bar harabar kotun. Sai sannan na saki ajiyar zuciya mai k’arfin gaske ina lumshe ido na. Duk wani bak’in cikin da ya cunkushe min a zuciya naji yana zagwanyewa. Yaya Usman bai tafi da ni gida direct ba sai da ya biya shop rite. Ya ce na zauna a mota ya shiga ya fito. Ya kai 1hour kafin ya fito da ledo di a hannunsa ya saka a mota. Sannan muka hau titi yana kallona ya ce “Gidanki zan kai ki ko gidan Abba?” Wani kallo na wurga masa sai kuma na saki murmushi na ce “Gida na kuma? Ai na bar gidan nan har abada Yaya Useey, kamar yarda na bar mai gidan, wancan karan ma ba yarda zan yi ne an fi k’arfina shi yasa na koma gidansa. Banda yanzu da na San ina da y’anci kowa kuma ya san ban aikata abinda na aikata ba.” Ya Usman ya waro ido ya ce “Ki bi komai a hankali AYSHA, me ye laifin Ustazun naki?” Na turo baki na na ce kada ka sake cewa Ustazuna Ustazun Hameeda dai.” Murmushi kawai ya saki bai musa min ba ya ja mota zuwa gidan Abba. Yana parking ya kalleni yana tsatstsareni da ido ya ce “Banda tuna baya, ki bi komai a sannu bana son rashin kunya balle ramuwar gayya.” Na d’an tab’e baki na kawai na fita daga motar. Shi kuma ya biyo ni da kaya a hannunsa. Fuskata a d’aure tamau na shiga gidan mu. Gaba d’aya suna tsaye a tsakargida da alama dawowata suke jira. Babu Wanda na kalla na yi hanyar wancan d’akin da suka bani lokacin da abin ya faru. Na shiga kai na tsaye. D’akin yana nan a gyarensa na dubi d’akin ina sakin murmushi da kai tsaye na San na takaici ne. Yaya Ysman ne ta turo k’ofa yana kallo na ya ce “Me ye haka AYSHA?” Na ware hannu na ce “Me na yi?” Tashi ki koma b’angaren Umma kiyi wanka a can.” Shiru na masa sai naga ya fita da sauri. Sai ga shi Sun dawo da Abba. Abban ma yana kallona ya ce “Shatu na me kenan? Tashi tashi don Allah, tashi ki koma cikin gida.” Bani da damar yi masa musu Amma ina ji a jikina wannan karan sai na d’ana. Kallonsa na yi da idona da yake cike taf da k’walla na ce “Abba ina zani? Nan d’in ai shine d’akina da kuka zab’ar min.” Gani na yi kawai ya zauna daf da ni, ya kamo yatsun hannu na cikin taushin murya ya ce “AYSHA banda tuna abinda ya wuce, komai ya faru a baya ina son ki d’aukeshi a matsayin k’addara, ba k’in ki ne ya saka muka yi Miki wancan talalar ba sai zallar soyayya, ba Wanda zai so yaga nasa a cikin waccan rayuwar. Wani gata ne bamu nuna Miki a gidan nan ba? Ina ji kaf yara na ba Wanda na so irin son da na Miki Shatu, to abinda aka ce kin aikata ne dole ya sosa zuciya dole mutum ya ji ba da’di a ransa duk mai sonki dole ya ji haushi amma ba tsana ba ce, mun yi haka ne don samun nutsuwarki AYSHA, tunda abin nan ya faru a kullum daren duniya sai na rok’i rabbil Izzati y’a shirya min ke, idan kuma bake kika aikata ba Allah y’a bayyana gaskiya…” kuka ne ya k’wace min na ce “Amma Abba me yasa baku yarda da ni ba? Me yasa ba ku yi tunanin a irin tarbiyyar da kuka bani ba zan iya aikata haka ba? Ya kamata tun a lokacin ku yi min uziri a yanayi na ya kamata ku San abinda zan aikata da Wanda ba zan aikata ba.” Ja na jikinsa Abba ya yi kawai yana bubbuga baya na. Cikin muryar lallashi ya ce “Ki yi hak’uri hak’ik’a mun yi kuskure…” Lunshe idona na yi a jikinsa ina tuna irin k’untata min da wulak’anta ni da aka yi, duk akan laifin da ba nawa ba. A kullum kallon tsana nake gani muraran a idanunsu. A hankali na ce “Ba wanda fa ya min uziri Abba sai Ya Usman Anty Khadija da Mami na, yanzu Abba da wani idon zaka kalli Mami na?” Sai naga ya runtse idonsa kawai yarda ya yi d’in y’a tabbatar min tabbas lamarin ya girmama a zuciyarsa cikin wata irin murya ya ce “Tabbas na zalunci Fateema, ban san kuma da wani ido zan kalleta ba, da ina da dama dana janyo wancan lokacin na goge abubuwan da suka faru a baya, sai dai lokaci ya k’ure min. Ayshatu na zalunceku don Allah ki yafe min…” sai naji Zuciyata ta yi rauni mahaifina ne ya zan yi da shi? Tilas na hak’ura Amma kam zan rok’eshi ya k’yaleni ba zan koma gidan Ustaz ba. Muryata na rawa na ce “Abba ka daina rok’ona wacece ni? Ni fa abar ikonka ce kana da dama a kaina zaka iya aikata fiye da hakan a kaina baka yi laifi a wajen Ubangiji ba, ballantana kuma ni, alfarma guda zan nema a wajenka don Allah kada ku matsanta min zama da Ustaz! Ina son ya sake ni.” Abba ya d’ago a hankali yana kallona sai naga ya girgiza kai ya ce “Me yasa AYSHA?” Bana son sa Abba a yanzu aurensa gaba d’aya ya fitar min daga rai, karatu nake son na koma, bana son na yi aure sai nan gaba.” Shiru Abba ya yi yana kallona kafin ya girgiza kai ya ce “Shikkenan, tashi yanzu muje ki yi wanka ki shirya a d’akin Ummanki, ga y’an uwanan fal a gidan suna jira ku ci abinci.” Na mik’e fuskata a dame da hawaye na bi bayan Abba. Har a lokacin suna nan a farfajiyar gidan mu. Ustaz yana zaune daga gefe idanunsa a kaina sai sakin mayalwacin murmushi yake. Ko d’igon fara’a babu a fuskata na shigesu na shiga d’akin Umma. Motsinta na ji a toilet sai gata ta fito tana sakin murmushi ta ce “Ayshatu kin shigo? To maza ki je ki shiga ki yi wanka na ha’da Miki ruwan wankan ki d’an rage kafin an jima ki je Saloon.” Cikin tausasawar murya take min maganar, sai na ji ta bani tausayi ganin yarda Har lokacin ta kasa sakin jiki ta ha’da ido da ni. Hakan yasa na fa’da jikinta na rungumeta sosai na sake kuka mai k’arfi sosai. Itama rungumenin ta yi tana sakin nata kukan da na tabbatar na abinda ta dinga min ne yake cin zuciyarta. Da k’yar na d’ago daga jikinta na zame na shige toilet. Wani irin wanka na yi da Har sai da na fara jin ra’dadi a fatar jikina sannan na hak’ura na bar dirzar kai na. Na yi sab’i ya kai ashirin gashin kaina kuwa ban san irin wankin da na masa ba har sai da Umma ta gaji ta fara buga min k’ofa tana kiran sunana. Hakan yasa na hak’ura na d’auro towel na fito daga toilet d’in. Umma na kallo na ta ce “Lallai kin dirzu AYSHA ji yarda fatar jikin ki Har wani ja take. Murmushi na yi na ce “Ba dole ba Umma, a sati fa sau d’aya suke bari mu yi wanka, wallahi ni kaina Har warin kaina na dinga ji.” Umma cikin tausaywa ta ce “Mun gode Allah dai da komai ya zama sai labari.” Zama na yi a gaban dressing mirror na shiga murtsike jikina da Neutrogena oil and body lotion. Ban yi wani makeup ba Umma ta kawo wata sabuwar riga light orange mai kyau sosai na zura a jikina. Da kanta ta min drying kai na ta gyara shi tsaf sai shinning yake. Gaba d’aya na ji jikina ya canja wata irin iska mai da’din gaske sai shigata take, kai Allah ya raba mu da k’addarar da zata kai mu gidan gyaran hali. D’ankwali na d’aura a kaina sannan na fita harabar gidan namu inda aka baza daddumai da tabarmi d’aya bayan d’aya na dinga gaisawa da jama’a kafin na zauna kusa da Anty Khadija da take fama da tsohon cikinta. Ya Usman ne ya yafito ni da hannu na mik’e na isa inda yake. A hankali ya ja hannuna ban san inda zai kai ni ba, na ga dai ya nufi d’akunansu da suke can daga gefe harabar gidan. Muna zuwa bakin k’ofar ya ce “Bana son musu AYSHA, ki shiga mijinki na nemanki.” Wani kallo na zuba masa na ce “Yaya Usman Miji kuma? Ai bani da Miji a halin yanzu…” kafin na rufe baki na ji an yi sama da ni ko ban yi magana ba na san Ustaz ne don naji mayataccen k’amshin turarensa….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 50….. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Shiru na mata kafin na tab’e baki na ce oho musu, ban san me suke nufi ba Mami, na dai ji Abba yana cewa yarinyar zata iya zama daga ahalinsu saboda matsananciyar kamar da muke, kuma ai kin ga masu kama da ni suna da yawa a dangi ko?” Murmushi na ga ta saki a hankali irin murmushin nan na gefen baki, ta ce “Ai kuwa masu kama da ke suna da yawa a dangi, zai iya yiwuwa y’ar wani ce a family.” Na ce “To Mami yaushe zaki dawo, tun da gaskiya ta bayyana?” Girgiza kanta ta yi ta ce “Ba rana AYSHA, kada ma ki sake min maganar nan, na bar gidanku har abada, wane irin cin mutunci ne Abbanki bai yi min ba da shi da zuri’arku gaba d’aya, Usmanu ne kawai bai zargeni ba don har nan gidan yazo yana bani hak’uri haka Ummanku ba abinda zan ce mata don ban ga alamun jin haushina a tattare da ita ba. Sai dai da yake ban san zuciyarta ba.” Shiru na yi na kasa cewa Mami komai, don ni da kaina shaida ce na San an ci zarafin Mami na, akan laifin da na tabbata bata ji ba bata gani ba.” Na da’de sosai don sai k’arfe uku na tafi, ina sake baiwa Mami hak’uri Amma ta nuna min sam ba zata hak’ura ba. Don ce wa ta sake yi AYSHA ni da gidanku Har abada.” Na mata sallama na tafi, ko ka’dan ban ga laifinta ba don ta k’i komawa gidan Abba don nima na sha alwashin ba zan koma gidan Ustaz ba, saboda irin maganganun da ya shak’a min masu kama da k’amshin mutuwa. Sanda na sauka har kusa da Mama na isa ina dariya na furta “Hajiya Mamanmu na tafi sai na dawo kuma? Ki dai daina cewa zaki zuba tsere da wannan gurguwar k’afar taki.” A fusace ta ce “Ubanki Imamu shine gurgu, jairar yarinya.” Na fice ina dariya abu na. A harabar gidanmu na tarar da dalleliyar motar tasa, sai walwali take. Tsaki na ja a zuciyata don na San shine saboda mayataccen k’amshin turarensa da na ji. A can gefe na hango su shi da Yaya Farouk. Tun daga nesan na ji kaifafan idanuwansa a kaina. Tsaki na zabga ina sake tsuke fuskata na shige su daga shi Har Yaya Farouk d’in ba wanda ya isheni kallo a cikinsu. Dalili suma su Yaya Farouk d’in Har yau ban daina jin haushinsu ba. Har na wuce Ya Farouk ya taso da sauri ya biyo baya na yana kiran sunana. Banda bana son na nuna masa raini a gaban Ustaz da ba zan tsaya ba. Sai da ya k’araso sannan ya ce “AYSHA kina kallon Mijinki kika share shi kika wuce baki tsaya kun gaisa ba, wannan fa ba tarbiyyar gidan nan ba ce..” wani kallo na watsa masa ina gani ya waro ido da alama mamakin kallon yake na kuwa tsuke fuska na ce ya je ya nemi matarsa, don ni ba matarsa ba ce na wuce tunaninsa.” Da haka na juya zan shiga gida. Ji na yi an ja hannuna an rik’e gam ko ba’a fa’d’a ba na San Ustaz ne daga jin yarda yanayin jikina ya sauya. Ga bala’in k’amshin sa da ya cika min ciki. Hannun na so na fisge sai dai ya k’i bani dama. Na juya a fusace ina masa wulak’antaccen kallo na ce “For the last time, malam na sake gaya maka kada ka sake rik’e min hannu…” Shima fuskarsa a d’aure ya ce “Da izinin wa kika fita? Da wannan gantalallen mayafin? Ko kina nufin don kin saka abaya shi zai baki damar fita ba mayafi da aure na a kan ki?” Tsaki na yi na ce “Na fita d’in, jikina ko naka? Sau nawa zan gaya maka kada ka sake kira na da sunan matarka, How I wish zaka iya ganin zuciyata kaga tarin tsanarka da take ciki…” Runtse idonsa Naga ya yi. Ya k’i sakar min hannun kuma a hankali ya bu’de idonsa da suka juya zuwa wani launi murya cike da kasala ya ce “You hated me but I love you AYSHA, na gode je ki gida.” Daga haka ya sab’ule hannunsa ya juya ya tafi. D’an tab’e baki na nayi duk da wani sashen na zuciyata yana son tausaya masa sai dai na k’i barin hakan ya yi tasiri. ————ZAMAN KOTU————- Ranar da za’a koma kotu da wuri muka tafi. Da kam na ce ba zan je ba, amma Ya Usman ya ce dole na ne na je. Ina kallo Umma jikinta a sanyaye take shiryawa har muka je kotun kuma yanayin walwalarta bai dawo ba. Mu ne a sahun farko a kujerun kotun. Fuskata sanye da bak’in glass kuma don na bawa Ustaz haushi yau ma ban saka Hijab ba, rolling na yi da mayafin abaya ta, na sha kwalliya a bina. Bakina har da chewingum ina tauna shi kamar da gayya haka nake satar kallon Ustaz yana ta zuban harara. Kotun ta d’inke da jama’a, kowa na son jin k’arshen shari’ar da zan kira mai sark’ak’iya. Ina ta hango Ahmad yana ta sakar min harara ni rabon ma dana gansa tun ranar da na gasa masa magana a harabar gidanmu. Ko waya ya daina yi min. Tsawon mintuna Ashirin muka d’auka kafin Alk’ali ya shigo aka buga gudumar kotu hakan ya bawa Kotun damar yin shiru. Aka kasa kunne saurarar Alk’ali. Su SHANY aka shigo da su kowacce sanye cikin dogon Hijab sai dai fuskokinsu a bu’de suke. Sai dai a fuskarsu zaka hango Sun rame ka’dan da alama a duk inda aka aje su basa jin da’di. Alk’ali ya kallesu d’aya bayan d’aya kafin naga ya gyara glass d’insa yana kallon lawyoyin da suke zaune kowa da takardu a gabansa. Alk’ali ya kalle su gaba d’aya kafin ya ce “A fito da Atine…” kowa ya zuba idon son ganin wacece Mama Atine. Kanta a k’asa ta fito tana yatsina fuska kana kallonta kaga cikakkiyar y’ar duniya mai ji da iskanci. Kowa zuba mata ido ya yi Kotu ta fara k’ananan surutai daga bakunan jama’a Wanda majority nasu tsinewa Atine ake. Ni kaina tsanar matar ce ta shiga zuciyata Farat d’aya na dinga Allah wadarai da ita. Allah dai ya shirya musulmi. Shi na ji Umma ta ce cikin raunanninyar muryar da ta saka ni kallonta da sauri. Alk’ali ya dubeta ya ce “Ke ce Atine Harka?” Ba tare da b’ata lokaci ba ta d’aga kai tana cije bak’in leb’enta. “Ni ce Atine.” Alk’ali ya jinjina kai ya ce “Ko zaki gaya min alak’ar ki da wa’dannan yaran? Kin san su?” Cike da confidence ta kalli Alk’ali ta ce “K’warai na san su…” “Menene ha’dinki da su?” Ta d’an tab’e baki ta ce “matsayin Uwa nake garesu tun daga jarirantaka Har kawo yanzu.” Alk’ali cike da mamaki ya ce “Matsayin Uwa? Kamar yaya? Kina nufin yaranki ne ko na y’anuwanki kike rik’o?” Anan kam tsit Atine ta yi, ta yi k’asa da kanta tana murza hannayenta alamar rashin gaskiya k’uru k’uru a fuskarta a zuciyata na ce Munafuka. Alk’ali ya girgiza kai ya ce “Atine, muna sauraron ki. Ko zargin da ake Miki ya tabbata ne kamar yarda yaran suka fa’da babu kowace alak’a tsakaninku dukkansu y’an tsintuwa ne?. Da sauri Atine ta d’aga Kai ta zubawa SHANY idonta da suka bayana tashin hankalin da take ciki. SHANY ta turo bakinta tana karka’da ido cike da tsiwa. “Y’an tsintuwa ne?” Muryar alk’alin da ya yi magana ta kara’de kotun Atine ta d’aga kai hankalinta tashe ta furta “Haka ne.” Alk’ali ya jinjina kai Kotu ta b’arke da hayaniya da k’yar aka tsawatar aka samu suka shiru. Alk’ali yana kallonta ya ce “Ikon Allah! A wani gari kika tsinci Har mutane 35? Banda wa’danda baa sani ba? Musamman waccan da tayi kama da wancan baiwar Allah. Don haka ake tunanin suna da alak’a mai k’arfin gaske, ko zaki gaya mana inda kika tsinceta?” Idonta ta kai kaina inda Alk’ali ya yi pointing da yatsarsa. Hankalinta tashe ta waro ido wani irin gumi ya dinga tsatstsafo mata. Alk’ali ya dubeta ya ce “Muna jin ki Atine kuma zancen gaskiya muke so. Sab’anin haka kamar kina rub’anya hukuncin da za’a zartar Miki ne. Gaskiyarki ce hanya mafi sauk’i da zata sauk’ak’a miki hukuncin kotu.. k’arya kuwa itace zata tsundumaki kogin nadama da dana sani….” Ido ta runtse tun daga nesa nake hango yarda k’irjinta yake hawa da sauka, murya a raunane ta d’ago idanunta da suka fara ambaliyar hawaye ta ce “Kamar yarda na fa’da, da gaske nake wasu tsintar su na yi wasu asibiti na same su wasu kuma siyar min aka yi….” ihu aka shiga yi a Kotun… da k’yar aka tsawatar “nima a k’ark’ashin wata mata nake, Wanda ita aikinta kenan safara da satar yara mata don tana fataucinsu zuwa k’asashe daban daban idan Sun girma. Asibitoci take bi wajen samun yara jarirai ko marasa galihu ta siya ko ta sata ko kuma wa’danda iyayensu suka Mutu ta hanyar accident aka rasa makusantansu Har gidan marayu tana ha’da baki da mutane ta yi adopting yara. Ni kaina a irin haka ta same ni, ma’ana ni shegiya ce. Duk abinda ta kashe maka kana yaro sai ta ninkasu sau d’ari kafin ta barka ka samu y’anci. Ko dai ta mayar da mutum karuwa ko tayi fataucinka zuwa wata k’asar. Idan kuwa shekarun tsufa suka zo maka sai ta sallameka kaima ka kafa naka gidan karuwan. Don tana fa’da ba’a aikin banza a kano. A irin haka ni ma na fito a cikin wa’danda aka sallama na kama gidan kai na sai na tsunduma irin harkar da take yi na shahara sosai Har na so na fita. A asibiti nake zagaye na siyo jarirai da ku’d’ade masu daraja a cikin k’asashen Nigeria. A irin haka wata rana yawo na ya kai ni jihar kano inda na isa Har asibitin Nasarawa. A ASIBITIN NA SIYO SHANY, hannun wata mata da ba zan tab’a manta fuskarta ba, ana ce mata FAD’IMA…… Daga Abba har Umma a wane irin firgice suke kallon matar Umma da k’arfi ta ce “Asibitin Nassarawa? Wane rana kuma wane kwanan wata? Tab gwarama! Wash Allah na na sha dogon typing don haka Har da na gobe🤣🤗. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[10/16, 5:44 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA…..51 NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Kotun zuwa lokacin tuni ta d’au hayaniya da cecekucen jama’a da suke ta yi ba k’akkautawa da k’yar aka samu bak’uncin shiru bayan buga gudumar Alk’ali. Umma a razane ta cigaba da kallon matar ita kanta bata San lokacin da ta yi wannan furucin ba murya a sama ta sake maimaita maganar tata, har sai da Alk’ali ya tsawatar mata. A hankali ta ce “A ranar lahadi 17 ga watan july 2000 wata irin razana UMMA ta yi tana nuna ta da yatsa ta furta “Na shiga uku, kada kice min wannan yarinyar jinina ce don ranar da na haifi Aysha kenan!” Gaba d’aya kallo ya koma wajen UMMA shi Kansa Abba jijjiga kai yake ni ma duk na bi na ru’de don exactly ranar da aka haife ni kenan. Alk’ali ne ya dakatar da Umma da take niyyar zuwa wajen Atine da k’yar aka samu UMMA ta zauna hankalinta tashe tana sake nuna Atine Harka. Ni kaina bugun zuciyata a lokacin ya k’aru sosai ba abinda nake sai zaro ido, glass d’in ma na ajiye sa. Alk’ali ya ce “Muna Jin Ki Atine wacece ta siyar Miki da Aysha?” Ta yi shiru har sai da ya sake daka mata tsawa sannan ta ce “Idan har ban manta ba sunanta Fa’dima ko Hajiya Fateema…” na dinga nanata sunan kamar mai son sanin ya ake fa’dar sunan, bakomai nake tsoro ba sai kada abinda zuciyata take tunani ya zama gaskiya, kada dai ace Mami na itace Fateemah da ake zargi. Ina ji UMMA a hankali ta ce “Ba yafiya tsakaninmu a wannan karan Fateemah matuk’ar na tabbatar da saka hannunki a cikin sace min jaririya.” Na d’ago ina kallonta itama na samu kallona take tana furzar da numfashi hankalinta tashe ta d’aga min kai. “Haka nake nufi Aysha, matuk’ar na samu Maminki ce da aikata wannan abin da gaske ba zan yafe mata ba, shari’a ni da ita har Kotun k’oli.” Zuciyata ta dinga wani irin tsalle cikin tashin hankali na dinga addu’a a raina kada Allah ya tabbatar da wannan lamari…. Alk’ali ne ya ce “A ina zamu sameta? Kafin mu ji su kuma sauran a inda kika samo su.” Ta girgiza Kai a hankali tana fincikar leb’enta ta ce “Ba zan ce ga inda take ba a yanzu dai kam, Amma idan na ganta tabbas zan shaida ta.” Bayan rubuce rubuce Alk’ali ya yi jawabi kamar haka. “Dole ne duk inda take ki gaya mana, kafin zuwan wannan lokacin za’a cigaba da rik’eki a kurkuku ba tare da zab’en tara ba. Samun matar da kuma zuwa asibitin wajen bincike ranar da aka haifeta da wacece ta haifeta idan ma baa samu Matar da ta siyar Miki ba na tabbata zamu samu record na wannan ranar In sha Allah.” Umma ta mik’e da sauri tana kuka ta ce “Wallahi ranka ya da’de y’ata ce wannan idan baku yarda ba aje asibiti a yi gwajin k’wayar halitta (Genetics) zaku tabbatar da haka.” Shiru Alk’ali ya yi kafin ya yi rubutu ya d’ago yana kallon UMMA ya ce “Duk wannan zai biyo daga baya, saboda kada ki manta har yanzu mai laifi ce ba zai yiwu mu naku ita ba. Alfarma guda zan muku shi likitan yazo ya d’ebi samples nata, da sauran duk abinda ake buk’ata aje a yi gwajin daga ranar da aka dawo kotu aka tabbatar taku ce za’a baku ita bayan hukuncin da Kotu ta zartar a kanta.” Jikin UMMA ya yi sanyi sai kallon SHANY take da dukkan idanunta da suka ka’da suka yi jajur. Ganin yarda hankalinta yake Neman fita daga jikinta sai kawai na damk’a hannunta cikin na Abba. Shi Kansa sam hankalin nasa kamar ya yi nisa daga jikinsa Amma haka ya yi k’ok’arin rik’e mata muka fita waje. Bayan UMMA ta sake fashewa da kuka ganin yarda aka fita da SHANY, itama Shanyn tana waiwayenta. Koda muka isa gida jikina a sanyaye nake jan k’afata. Bakomai yake dagula min lissafi sai tunanin MAMINA. Fatana kada Allah yasa Mami tana da hannu a cikin wannan abin da zan iya kira son zuciya. A raba d’a da Uwarsa a ranar da yazo duniya…. Idan har ya zama da saka hannunta a ciki ya makomar Mamin zata kasance? Wasu hawaye masu zafin gaske suka dinga bin idanuna. ★★★ Haka na kwana da zancen a zuciyata. Da safe ko karyawa ban yi ba na nufi Umma da zancen. Da ido ta dinga bina da kallo kafin ta saki ajiyar zuciya ta ce “Tunani na yazo d’aya da naki, da na Abbanki ma duka. Shima zargi da hasashen da yake kenan. Sai dai zan kwab’eki kamar yarda shima na kwab’eshi. Kada ku kuskura ku furta wannan zancen ga kowa har sai gaskiya ta bayyana, kada a zo a sake jin kunya don ba lallai ne abinda muke tunanin ya zama haka ba. Amma ya rantse wannan karan idan ya samu Fateemah ce silar salwantar yarinyar sa ba zai yarda ba sai ya yi shari’a da ita. Ba zai mata sassauci ba. Burinsa kawai a yi gwajin k’wayar halitta ya samu k’wakwkwarar shaida a kotu…” A hankali na ja numfashi na fesar murya a raunane na ce “Kai jama’a! Wallahi duniya abar tsoro ce.” Umma ta jinjina kai kawai. Na gyara zama na ce “Umma don Allah zan je gidan Ahmad akwai wasu kaya na da books da nake son na d’auko.” Ta d’an kalleni kafin ta ce “Ahmad d’in ai yana nan gidansa mai kallon gidan nan, ki masa magana mana ya kawo miki, balle ma meye na d’ebo kayan ke da zaki tattara ki koma gidanki, ko shikkenan kina nufin kin barwa Kishiyarki Mijinki kenan?” Na turo baki na kamar yarda na Saba ya zame min jiki na ce “Ni fa Umma ba zan koma ba, don Allah ki bar ni na je yanzu zan dawo.” Ta d’an kalleni sai kuma Naga ta saki ajiyar zuciya ta ce “Ai shikkenan, sai ki buga waya ki sanarwa Mijinnaki ko ki gayawa Abbanki zaki fita don ni dai ba zan baki izini ba kin sani.” Na marairaice fuska na ce “Allah Umma yanzu zan dawo. Baba driver ne ma zai kai ni.” Umma ta kafe ba zan fita ba sai na sanar da Ahmad ta mik’a min wayarta “Maza ki tura masa text, ai ba a garin mahaukata muke ba.” Dole na tura masa message. Sannan Umma ta barni na fice da sauri. Ko Drivern ban nema ba, don ba gaskiya na gaywa Umma ba, ba wani gidan Ahmad da zani gidan su Mami na zan tafi. Na k’agu an gano koda. Saka hannunta a ciki. Wannan karan Mama da fara’a ta tare ni Har mamaki abin ya bani. Duk wannan d’acin ran da bak’in ciki Babu shi. Mami na kuwa tashi ta yi ta rungumoni sosai jikinta tana furta “Oyoyo Ayshatu na.” Ni dai murmushin yak’e kawai nake saboda yarda zuciyata take dukan tara-tara. Daga haka Mami ta jani cikin d’akinta har da turo k’ofa muka zauna a gefen gado. Kawai na ji Mami ta jefo min tambaya. “Ayshatu y’a aka k’are da zaman kotu? Wannan karan ai k’in zuwa na yi tunda Naga kin yi free na ce me zan je na yi..” D’an murmushi na jefeta da shi. Zuciyata na sake kambama zarginta da nake. Murmushin nawa San bai kai zuci ba na ce “Ai kuwa Mami da kin sha kallo, SHANY dai ana zaton ni da ita Twins ne, don rana guda aka haife mu, a kuma asibiti guda…” Da sauri Mami ta zaro ido ta ce “In ji Uban wa kuma?” Na gyara zama cike da mamakin firgicin ta na ce “In ji matar da ta raine su ita ta fa’di inda aka yi tazo hannunta, matar ta tabbatar da cewa siyanta ta yi a asibitin bisa jagorancin wata mata…” A hanzarce ta ce “Wata mata kuma? Wacece ta fa’di sunanta?” Na yi shiru ina nazarin yanayinta kamar dai tun yanzu zuciyata na son tabbatar min da zargi na. Na jinjina kai na ce “Ta fa’da mana, sunanku d’aya da matar da ta ce ta yi hanya an siyar mata da y’ar.” Wani irin kallo naga Mami tana min kafin ta mik’e tana zagaye d’akin hannayenta sak’ale da bayanta. Jikina ya yi sanyi k’alau ko Mami bata fa’da ba na San tana da hannu dumu dumu a cikin wannan lamarin. Wata k’walla ta kawo ido na. Na mik’e ina d’aukan handbag d’ina. Na k’arasa gabanta idanunta a lumshe suke na ce “Mami zan wuce.” Da k’yar ta bu’de idanunta da suka juye lokaci guda ta d’an lashi leb’enta ta ce “Ki gaida gida AYSHA.” Ta fa’da da wata irin murya da na rasa yarda zan kwatanta. Ina fita na ratsa bayan gidansu Mami na zauna na ci kuka na sosai don na San Mami ce da wannan laifin bana haufi. Sai da naje k’ofar gida Sannan na tuna k’arya na shiryawa Umma akan zan je d’ebo kaya. Hakan yasa na juya na nufi gidansu Asma da sauri. Ashe rabon na yi mugun gani don Ustaz na gani tsaye da zank’alak’ok’in matarsa a daidai k’ofar gidansu da alama fita za su yi. Muka yi four eyes da shi. Wani abu na ji ta tokare min k’irji. Na zabga masa harara na shigesu ba tare da na musu magana ba. Muryarsa na ji a daf da ni yana furta “Ban yafe fitar da aka yi ba da izini na ba.” A masife na juyo na masa wani irin kallo mai nuna bala’in da zuciyata take ciki ba. D’aga min gira ya yi yana lumshe ido ya ce “Abinda na ce kenan Mara kunya.” Wani yawu mai d’aci na ha’diya na kasa furta masa komai saboda takaicin da yake cike da zuciyata. Kuma muddin na tsaya zan iya saka masa kuka a wajen ni kuma ban shirya zubar da aji na ba. Don haka na wuce fuskata a d’aure na fa’da gidan su Asma. Ina jin zuciyata kamar ta fito don tsananin zafin kishi tabbas na yarda da gaske kishi masifa ne, don haka na sake damk’e wa a raina ba ni ba gidan Ustaz Har abada. Da na koma gida Umma bata ce min komai ba ganin kaya na da gaske a hannu na. Bayan kwana biyu. Sai ga Abba ya shigo gida a yammacin ranar hannunsa d’auke da takarda ya same ni da Umma a kitchen ya mik’a mata ta dubesa da sauri ta ce “Na menene?” “Result d’in genotype ne ya fito…” Hannun Umma na rawa ta fara bu’de takardar….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….57. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Akwai a arewabooks masu nema dafa farko. Wata irin fa’duwar gaba ce ta same ni, fa’duwar gabar da ta saka ni jin matsanancin ciwon kai. Na kasa gane a wani mahalli zan saka abinda Abba ya ce. Tashin hankalina bai sake yawaita ba sai da Naga Ustaz ya zato jotter da biro da alama cika umarnin Abbà zai yi. Tsaf na daina fahimtar abinda ake cewa Amma miskilancina ya kasa bari na na ‘d’ago na ce wa Abba na janye buk’ata ta. Ina kallon Ustaz kuma ya yi rubutun fuskarsa d’auke da wani yanayi da na rasa mahallin da zan ajiye shi farin ciki ko bak’in ciki. Ya mik’awa Abba takardar yana furta “Ku taya ni murna y’an uwa da karamcin Abba ba abinda zan sakawa da Abba da shi sai addu’a. Abinda ya yi AYSHA Ai shi ya yi Humaira kamanninsu guda ba wani banbanci na gode sosai.” Abba ya ce “Bakomai Ahmadu, ka cancanci fiye da haka, sam ba zan so na rasa ka cikin zuri’ata ba. Allah ya yi muku albarka.” Tamkar wani magana’disu haka idanuna suka game da idon Ustaz kawai sai naga ya d‘aga min hannu ya saki murmushinsa mai kyau. Da alama manufarsa sai wata rana. Zuciyata ta buga da k’arfin gaske wannan shi ake kira da yiwa kai Me na janyowa Kaina Ni AYSHA? Ina miskilanci na ya kai ni yau? Jikina a salub’e na mik’e Har jiri nake ji na shige gida zuciyata na harbawa da saurin gaske. Zuciyata a cunkushe da tunani ina tunanin tabbas wata mak’ark’ashiya Ustaz ya shirya min. Wato yaga Humaira ta fi ni wayewa ta fini faran fatan shine dalilin juya a kalar soyayyata zuwa tata. Sam bana ganin laifin abinda na aikata ni balle na hango kuskurena. Don kuwa ko sonsa zai kashe ni sai dai ya kasheni don ba zan tab’a nuna masa na damu koda hakan zai zama Ajali na tabbas miskilanci bai yi ba. Wani irin yawu na ha’diye mai kaurin gaske, sai a sannan hawaye suka shiga suntiri a k’uncina. Na fara kamar jin haushin Humaira da tsanarta a zuciyata tamkar laifinta ne, tamkar ita ce ta ce tana son sa. Kowa ma na gidan haushinsa nake ji tuni dama na yarda Umma tafi son Humaira a kaina don yanzu janta da take a jiki na bata ja na. Ni kam ai na yi rashin mai k’aunata Mami na. Na zaro waya da sauri don kiran Mamin nawa amma still wayarta not reachable hakan yasa na mayar da alamar kiran nawa zuwa Mamanً ta. Ta d’aga muka gaisa na tambayeta Mamin nan take sanar da ni ta wuce England karatu kwana biyu da suka shige Amma zata turo min numberr da ake samunta ta can.” Jiki na a salub’e na kashe wayar ina goge zufar da na ji tana tsatstsafo min a goshi na. Ashe wancan lokacin ban ga komai ba yanzu ne NA GA RAYUWA NI AYSHA. Har dare ban fito ba haka na kwanta da yunwa ruwan tea kawai na sha. Ba Wanda ya nemeni har Umman. Da Humaira da Khadija da Maryam muke kwana d’aki d’aya wani lokacin Humaira ta gudu d’akin Umma. Su kuma sauran biyar d’in suna d’akinsu da yake b’angaren Mami. Har asuba ranar ban yi wani barcin kirki ba, ina salloli. Shi yasa da barcin ya d’auke ni y’a d’aukeni da k’arfin gaske. Hayaniyar su ce ta farkar da ni daga nauyayyan barci kaina na ji ya sarà ganin yarda suke ta hayaniya suna shiryawa. A tsawace na ce “Malamai kun dameni fa, kun hanani barci.” Humaira da tsallenta ta dirò saman gadon tana jan bargon. Cikin masifa na ce mata “Ke meye haka?” Langab’r kai ta yi. Kafin ta furta “Sissy, kin manta da batun zuwa potiskum d’in, ki shirya kada Su Yaya su tafi su barki ni a motar Ustazu na zan tafi.” Wani kallo nake mata ina jin kamar na k’unduma mata zagi wato da iskanci ma da sunan da nake kiransa take kiransa. Sai dai na ha’diye ina jan tsaki na ce “ku je kawai, ni ba zan je ba.” Bata ce komai ba ta fice daga d’akin. Tsawon lokaci sai gata Sun dawo da Umma. Umma ta kira suna na ni kuwa na yi shiru kamar mai barci. Sai na ji ta ce “Humaira mu je barcin ne a kanta. Sa zauna da masu aiki.” Na bi bayan Umma da suke ficewa daga d’akin da kallo. Wato abinda na lura da shi sam Umma bata damu da ni ba balle ta tambayeni damuwata. Na datse leb’ena ina jin raunin zuciyata na sake rub’anya. Na mik’e a hankali na shiga toilet wanka na yi sosai kafin na fito na hau shafe shafe a jikina. Abinda ban cika yi ba yau nice har da kwalliya ba don komai ba sai don na burge Ustaz, don ban ban sani ba ko kwalliyar SHANY tana daga abinda yake janye hankalin Ustaz d’in. Na shirya cikin black abaya mai masifar kyau kalar kuma ta amsheni sosai kalar light pink da adon black stones a jikinta. Ni kaina na San na yi kyau ba d’an ka’dan ba. Fuskata kuwa sanye nake da wani black shade da ya sake fito da kwalliyar tawa. Ni kaina sai da na sake duban kaina a mudubi kafin na saki murmushi don na San ba Ustaz ba duk Wanda ya ganni sai ya yi mamakin kwalliyar da na zauna na rincab’a. Ina fita kuwa suka zuba min ido suna furta Wow Ma sha Allah. Na d’an d’aiuke kaina bakina nake d’an motsawa ina tauna chewingum d’in da yake cikinsa. Motar Ya.Usman na bi, don ko da wasa nan nufi motar Ustaz ba. Jan aji da shan k’amshi na ba zai bar ni na aikata hakan ba. Shima ina kallo sau ‘d’aya ya kalleni bai sake ba, Ya tattara dukkan nutsuwarsa ya mayar kan Humaira da take ta masa surutu da dariya shima kuma ina kallon yana mayar mata da murmushin kamar dama jira yake. Na shiga Motar Ya Usman zuciyata na min wani irin nauyi, don har sai da na sauke ajiyar zuciya a hankali. Yaya Usman ya juyo yana kallona bayan ya tada motar ya ce “Yaya dai AYSHA?” Na girgiza kai na ce bakomai. Ina bayan motarsa matarsa kuma a gaba haka muka yi tafiyar. Ina ji jefi jefi suna hirarsu wani zubin su sako ni. Sai dai bana tofa musu na yi shiru kawai saboda tunanin da y’a cika min zuciyata ba zai bar ni na yi walwalar da zan amsa musu ba. Har muka isa potiskum ban sani ba ni dai ina zaune jigum cikin mota duka tunani na yana kan motar Ustaz da duk sanda muka zo wuce su sai na hango fuskarsa da ta Humaira fal farin ciki da walwala. Bayan motarsa kuwa Yaya Muhammad ne da Anty Khadija da ta kafe sai tazo duk da tsohon cikin da take da shi. Mune farkon isa potiskum d’in don haka Hajiya da murna da karsashi ta tare mu. Ta dafa ni ta ce “Kaga Baiwar Allah, tun d’azu nake zuba idon ganinku ina y’ar Uwar taki?” Kafin ta rufe baki Humaira da su Umma suka shigo. Hajiya ta bu’de baki cike da mamaki tana furta “Hukumullahi La ajabun…. Ikon rabbi ya shige misali wannan kam ko a hanya na ha’du da ita zan k’walla mata kira da sunan Ayshatu. Ki ga kama ba banbanci ko ka’dan…”Umma tana dariya ta ce “Aa fa Yakumbo akwai banbanci na ‘dabi’a a tattare da su, Humaira akwai d’an banzan rawar kai, da yawan surutu Aysha kuwa miskila ce ta bugawa a jarida.” Ina ji duka wajen suka shiga furta tabbas. Na d’ago ina kallon Ustaz da sam bai tofa ba yana ta danna wayarsa. Ya Muhammad ya ce “Wallahi gaskiyarki Umma, Humaira akwai sakewa da jama’a Aysha kuwa akwai nurk’ifanci.” Na turo baki na cikin jin haushi ina kallon Abba da yake murmushi shima ya ce “Humaira kam ba dama surutu fa kamar aku.” Ai kuwa Humaira ta fara turo baki tana shirin saka kuka, Yaya Faruk y’a kama hannunta yana furta “Common my friend, kada kiyi asarar hawayenki a banza, ai gwanda mai irin halinki Sun fi da’din zama. Me za’a yi da mutum mai k’unbiya k’unbiya.” Na kuwa zuba masa harara don na San wannan maganar kansa tsaye da ni yake. Kwana guda muka yi a potiskum muka yi sallama da Hajiya da niyyar ana fara shirye shiryen biki zata taho. Kwana biyu da dawowarmu kuwa aka fara hada hadar saka rana. Wani abu da Abba ya yi ya burgeni ha’da su Yaya Muhammad su biyar da biyar daga cikin y’an matan nan. Masu mata ya k’ara musu d’ai’daya marasa mata kuma ta basu auren d’aid’aya daga cikinsu. Yaya Ali ne kawai aka ce ya yi k’ank’anta da aure don haka sauran biyun Malaman mu suka nemi aurensu Abba kuma ya amince da su ya basu auren don haka duka yau za’a saka ranar biki ciki kuwa har da na Humaira da Ahmad Ustazu na. Ranar kam Allah ne ka’dai ya san yanayin da zuciyata take ciki. Duk da k’wayar idanuna ta kasa b’oye nakasar da zuciyata take ciki. Y’an saka ranar da suka zo Har da y’an gidansu Ahmad su Khadija da Aunty Doctor Khadija ta saka ni a d’aki tana tuhumata me yasa na k’i amincewa komawa gidan Ahmad? Suka ji labarin da k’anwata kuma za’a yi auren. Na bita da kallo ina sakin ajiyar zuciya kafin na ce “K’addara ce!” Duk abinda ta ce kuma na kasa bata amsa Har ta gaji ta yi shiru. Zo kuga lefen Humaira, akwatina goma sha biyu har da na saka rana. Akwatina ne manya kuma masu masifar kyau. Kaya ne damk’ar a cikinsu masu masifar kyau da tsada. Kai daga gani ka San dukiya ta yi kuka. Wata uku aka saka cif. Humaira sai rawar kai take ita ko kunyata bata ji. Wannan iyayi da take shine abinda yake sake dugunzuma zuciyata. Hakan yasa na shige d’aki na fasa kuka mai tsima zuciya. A wannan daren kam cire duk wani girman kai da miskilanci na na yi na d’au waya na danna numberr Ustaz, yarda wayar take bugu haka k’irjina yake bugu sosai na tashin hankali tsawon lokaci kafin ta d’aga wayar……. Cikin k’arfin hali na furta “Hello Ustazu na….” 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA…..58. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Na fa’da a hankali cikin muryar nutsuwa. Shiru ya yi kafin daga can gefen ya ce “Humaira me yasa kika d’aukar wa AYSHA waya?” Wani takaici ne da zafin k’irji na ji yana shirin babbaka zuciyata wato ya zata Humaira ce. Na cije leb’ena kafin na yi k’asa da wayar jin yana cewa “Maza Humy mayar mata da wayarta zan shigo da safe na ji damuwarki yanzu Am with my wife…” k’it na kashe wayar tafarfasa kawai zuciya ta take yi. Ban san me yasa na kasa hak’ura da Ustaz ba, alhali yanzu ta bayyana k’arara ba so na yake ba. Hankalinsa da tunaninsa kacokam yana kan Humaira. Ranar kam da ky’ar na samu na yi barci. Da safe kuwa ban fita daga d’akin ba. Maryama ta shigo tana kallona ta ce “Sis AYSHA Abba yana kira.” Kai kawai na d’aga mata kafin na mik’e na zira hijab d’ina na fice zuwa amsa kiran Abba. Ina saka kai gaba na na wani irin bugawa da k’arfin gaske ganin Abba ne da kafatalin y’an uwansa da alama wannan meeting d’in duk nawa ne. Kai Ni AYSHA na ga rayuwa. Cikin rawar murya da kasalar jiki da na zuciya na shiga babban parlorn kai na a k’asa. Fuskarsu sam ba annuri suke kallo na. A takure nake sosai musamman irin kallon da suke min mai sanya rashin nutsuwa ko ka’dan. Bayan Sun amsa gaisuwata Usual murya a cunkushe sai kuma Baba Yahya ya gyara zama yana furta “Ke wannan zaman naki ne, saboda wata magana da muka ji wai zaki jingine maganar aure ki tafi wata uwa duniya karatu, haka ne?” Na d’aga kai a hankali ya gyara zamansa ya ce “To baki isa ba, kin yi ka’dan mu dai a zuri’armu kaf ba wata mace da zamu bari ta tafi karatu waje. Don haka ki bu’de kunne da kyau mu gaya Miki da zarar kin gama idda zaki fitar da miji mu Miki aure tunda ke kin kafe ba zaki koma gidan mijinki ba, har ta kai ga rabuwa an Maye masa gurbin ki da y’ar uwarki to hakan ba zai baki lasisin da zaki zauna ki mik’e k’afa ba.” K’asa furta komai na yi sai ruwan hawaye da yake ambaliya a fuskata. A haka suka sallame ni na mik’e jikina har rawa yake na tafi cikin d’aki na. Zuciyata na ke furta na shiga uku, na jawowa kai na masifa me ya kai ni furta bana son Ustaz na San halin su Baba yahya da kafaffiyar zuciya. Tunda suka furta sai na fitar da Miji abu ne mawuyaci su janye furucinsu. Kaina ya yi dum, sakamakon rasa mafita da na yi, a lokacin kam na San tabbas na yi rashin uwa Mami na da ta nan da na San ba zata bari a k’wace min Miji a bawa Humaira ba. Ita kuwa Umma murna ma take don k’iri da muzu ina jinta ranar tana gayawa K’anwarta ita hankalinta ma zai fi kwanciya Humaira ta auri Ustaz ta San zai kula da ita da tarbiyyarta ma. Na runtse idona hawaye na zuba kamar da bakin k’warya a idona. Numberr Mami na shiga latsawa ta can k’asa da Hajiya Mama ta bani. Cikin sa’a na samu Mami na, tana d’agawa na fashe mata da kuka ina furta “Mami na shiga wani hali, Na ga rayuwa Mami na wai Humaira za’a aurawa Ustazu na…” “What? Saboda Uban me?” Na ji Mami ta furta cikin muryar da ta bayyana tashin hankalinta. Na lumshe ido ina gaya mata duk abinda ya wakana. Sai na ji ta saki ajiyar zuciya ta ce “Ke ma AYSHA kin yi wauta, a wannan zamanin ta ya zaki furta hakan? Ustaz fa maza ne masu tsada da sai mace mai muguwar sa’a take samunsu. Ko da da kika ga ina Adawa da aurenki da Ustaz don bani da wani burin da ya wuce naga kin yi karatu ne. Amma na San ta ko ina Ahamad ba shi da makusa. Yanzu wannan nurkufancin naki zaki cire ki samu Umma ki gaya mata kina son mijinki zaki koma gidansa ita sai ta samu Abba ta gaya masa amma idan kika ce zaki shiru kina ji kina gani zaki rasa Ahamad Humairan ta aure shi…” na d’aga kai zuciyata ta amince da shawarar Mami na. Na mik’e da sauri na nufi d’akin umma. Ita da Humaira ne a zaune Humairan sai sangarta take mata. Kayan kitchen ne a gaban su suna ta warewa. Jikina a sanyaye na shiga na zauna a gefen gadon, ina nazarin fuskokinsu da suke cike fal da walwala da alama koma zancen me suke suna cike da nisha’di. Umma ta d’an kalle ni tana furta “Ayshatun Mami ya aka yi ne? Akwai matsala?” Na d’aga kai kawai ina wasa da yatsu na na ce “Ina son magana da ke Umma.” Umma ta d’an dubeni tana duban d’akin kuma sai ta ce “Yi maganar ki mana, ai ba kowa ni da y’ar uwarki ne kawai kuma bai kamata ace kina b’oye mata abinda ke ranki ba, duk duniya baki da makwafinta.” Na d’ago ina kallon Humaira da itama take kallona tana sakin murmushi a hankali. Sai kuma Naga ta mik’e ta yi pecking d’ina a kumatu ta ce “Feel free Sis ki gayawa Umma matsalarki she is ur mother baki da misalinta, bari na baku guri.” Bata jira cewar Umma ba ta fice da sauri. Na saki ajiyar zuciya ina kallon Umma da ta kafa min ido. “Ina jin Ki Shatun Mami, me ya faru?” Na yi k’asa da kaina cikin rawar murya na ce “Mhmn, Umma dama maganar Ustaz ne na amince zan koma gidan sa a bar maganar aurensa da Humaira.” Wani irin kallo na ga Umma tana min bakinta a sake da alama mamaki ne fal a zuciyarta ta ce “AYSHA wace irin magana nake ji, Mara da’din ji haka? Me yasa kike son mayar damu k’ananan mutane? Da kanki fa kika ce ba kya sonsa sai yanzu da Har ya kawo lefen y’ar uwarki da saka ranar aurensa sai kuma ki ce shi kike so. To wannan maganar ta tsaya tsakanin ni da ke kawai bana son ko a zuciyarki ki sake maimaita ta. Ahmad shi ya dace da auren y’ar uwarki ko ba kya son ya zama silar gyaruwar dukkan laifikanta. Kada ki zama mai son kanki mana Ayshatu.” Ta dafa hannuna ta ce “Ki yi hak’uri kina gama idda ke ma zaki samu mijinki ki tuna ita zata yi wuyar samun miji musamman irin rayuwar da tayi a baya, tunda yanzu kuwa Allah yasa babban Malami irin Ahmad zai aureta ai sai mu godewa Allah ke kuwa na San zaki iya samun kwatankwacinsa ko Wanda ya fi shi In sha Allah, tunda ke baki da wani aibu…” Zufa ce kawai take fita daga jikina. Na dinga kallon Umma ina mamakin kalamanta. Anya kuwa Umma na so na? Ko dai Har soyayyar uwa ta tattara ta barwa Mami ni. Idona suka ka’da suka yi jajur ina jin yarda jijiyar kaina take harbawa da k’arfin gaske na runtse ido na ina ji Umma ta d’an rungumeni ta hau bubbuga kaya na. A hankali ta ce “Ki zama mai son y’ar uwarki fiye da kanki AYSHA, ke kin taso da gatanki ita kuwa fa? Kinga dole yanzu tana buk’atar kulawar mu da dukkan soyayyarmu.” Ban amsa mata ba. Kukan ma kuwa ya k’i zuwa sai zugin zuciya da tsananin b’acin rai. Na janye jikina na mik’e kawai ina harha’da hanya na bar d’akin. Kashe wayata na yi gaba d’aya na daina kula kowa a gidan kullum cikin shiru nake hakan kuma bai saka Sun fasa shirye shiryen biki ba. Wanda zai zama daidai lokacin da na gama Idda. Ranar da naga period d’ina na k’arshe hankalina ba k’aramin tashi ya yi ba. Don na San ni da Ustaz kuma sai gani sai hange daga nesa. Hakan ya tashi hankalina sai dai na tattara na mik’a lamari na ga Allah. Na tabbata tawa k’addarar ce haka. Mami na ma ban sake nemanta da zancen ba. A ranar da zan yi wankan tsarki na gama period kasa yin wankan na yi saboda matsananciyar fargaba da b’acin rai. Na yi wata irin rama da ko lokacin da abubuwan can suka faru ban yi ta ba. Fuskata baka ganin komai sai idanuwa. Na kasa samun nutsuwa Har sai da na danna kiran Mami na. Bugu guda kuwa ta d’auka tana furta “A’in Mami ya aka yi?” Na fashe ina gaya mata na gama idda yau. Shiru ta yi kafin ta saki ajiyar zuciya ta ce “Ustaz ya san kin gama ko zaki gama a yau?” Cikin kasala da mutuwar jiki na ce “Na san ya sani don kwanakin period d’ina a kansa suke kamar yarda duk zan fara period shi yake gaya min yau Madam fa sai a hankali bak’o zai zo.” Mami ta yi shiru kafin ta ce “AYSHA, yanzu ba abinda ya rage mana sai ki fito musu ta yarda suke so, da zarar sun Miki maganar fito da miji ki ce kawai kin bawa Abbanki wuk’a da nama na San zai gane kina son komawa auren Mijinki ne, shikkenan sai ki a mayar da aurenku.” Na saki ajiyar zuciya ina jin shawarar Mami accepted har cikin rai na. Da sassafe kuwa da kaina na shiryawa Abba favorit food d’insa Masa da miyar taushe. Duk ba na komai bane sai na cin hanci. Na dama masa kunun gya’da ha’dadden ba abinda yake sai k’anshin gya’dar gashi fari tas kamar yoghurt. Har a Sallahr walaha sai da na rok’i Allah yasa Abba ya amince da abinda zan je masa da shi. Ina kallo Su Humaira kallona kawai suke yi, sai dai ba su min magana ba don yanzu na zame musu horror komai suka yi masifa nake musu. Da kaina na kinkimi kwandon Abincin Abba na shiga da shi parlorn a raina ina furta “Yairinya kwalelenki, mijina yafi k’arfinki ko ta halin k’ak’a sai na k’wato abu na.” Har k’asa na kai na gaida Abba da yake ta kallo na yana furta “Yau A’in Mami ta tuna da Abbanta kenan, Har gashi an min delicious.” Na yi k’asa da kaina ina murmushi ganin fuskar Abban fal nisha’di da alama hak’ata zata cimma ruwa. Abba ya ce “Ko an samo min surikin ne? K’in ga shikkenan sai a ha’da da na y’an uwanki don na San yanzu dai k’in gama idda.” Na girgiza kai na ina murmushi na ce “dama akan maganar na zo Abba.” Ya gyara zama yana furta “Alhamdulilah, addu’a ta ta amsu kenan, yaushe suka ce zasu turo?” Idona ya kawo ruwa sosai kafin na d’an girgiza kaina cikin k’arfin hali na ce “Abba, na baka zab’i ka zab’a min duk Wanda ya maka ni kuma zan aure shi.” Abba ya saki murmushin jin da’di ya ce “Kin tabbata AYSHA? Ko wa na baki zaki amince ki aure shi?” Na d’aga kai da sauri. Sai na ji ya ce “Alhamdulillah da y’a ta gari, ina alfahari da zamowar ayshatu cikin zuri’ata, Allah ya Miki albarka ki shirya yau da daddare zaki yi bak’o.” Duka k’irji na yake yi sosai na mik’e a kasalance na mik’e na fita. Sam ba haka na so na ji Abba ya ce ba, so na yi ya ce shikkenan AYSHA za’a mayar Miki da aurenki da mijinki. Duk da haka nan cire rai ba, ban sani ba ko akwai wani suprise da Abba yake min, may be da daddaren Ustazu na zan gani a zuwan Wanda ya zab’a min. Don haka har dare na kasa samun nutsuwa duk da haka na fece kwalliya sai zabga k’amshi nake sabuwar atamfa na saka mai masifar kyau na yafa babban mayafi da niyyar ina shiga wajen Ahmad zan cire mayafin tunda Naga yanzu hankalinsa na kan wayayyun mata. Kaina dama ko d’ankwali babu gashi na ne na gyara shi sosai ya kwanta abaya na. Ai kuwa Maryam na zuwa ta ce min ina da bak’o na mik’e. Kitchen na shiga na d’au tray d’in da na ha’da masa delicious a ciki. Na saka kai na a parlorn. Zuciyata ta yi wani irin bugawa ganin Wanda yake zaune ban san sanda na saki tray d’in ba, kayan ciki suka tarwatse a k’asa gaba d’aya….. 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….60. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Don haka bana so na sake Jin kin furta kina son Ahmad, balle wani ya ji a yi da mu. Ki rungumi Mijinki ki so shi, sai ki ga watarana kin yi alfahari da aurensa balle yana son ki kuma shima yana da rufin asiri fiye da Ahmad ma.” Wasu hawaye kawai na ji Sun ziraro min na kasa furta kalmar komai sai ajiyar zuciya nake saki. Umma ta ce “Ke ai gaba ta kai ki, irin wa’dannan mutanen da suke ninka ka a shekaru Sun fi iya lallab’a mace da nuna mata tattali, don Allah Ausha ki so Abin ki ki bashi dukkan kulawa…” zaro ido nake kawai, ina tunanin ta ina zan fara son wannan abin? Ta ina zan bashi kulawar? Da wani rungumemen cikin za’a sha soyayyar. Ni AYSHA mai mafarkin auren Miji d’an gayu sai na b’ige a Mamuda mai tumbin ku’di. Na San su Asma zasu sha dariya don na sha alwashin ba zan auri mummunan mutum ba ko mai ku’dinsa kuwa gara na auri kyakykyawan da bashi da ko sisi. Umma bata sake bi ta kaina ba ta dai dafa kaina ta d’an shafa alamar rarrashi ta fice daga d’akin. Ni kuwa bin bayanta na yi da kallo ina tunanin yarda Umma ta zamo uwa a gareni Amma bata damu da ni ba, bata son farin ciki na. Ban sani ba ko sanda ta bawa Mami ne Har duk wani so da tausayi irin na uwa da take min ta tattara ta barwa Mami. Za’a sha drama don ba zan yarda da auren Mamuda ba. Haka aka shiga gudanar da shagulgulan biki, ni dai nawa ido don bani da wata mafita kuma banda Allah. Har Anty Khadija da take fama da jeho bata zauna ba a bikin nan sai kai da komowa take tun tana bani hak’uri Har itama ta gaji ta tattara ta zuba min ido. Gyaran jiki kuwa haka na hak’ura ina ji ina gani aka gurji jiki na. Bana fita ko ina abinci ya zama bak’ona ruwan shayi kawai nake sha shima sai na runtse ido. Yaya Usman tun yana bani hak’uri har ya tattara ni y’a watsar. Y’an matan Umma kam an sha kyau na ban mamaki ina kallo aka kawo lefen Humaira daga gidan su Ustaz akwati na sha biyu. Ranar da ya kama za’a kai amare. A ranar na ji labari wajen Anty Khadija wai nima zan bi Mijina Abu Dhabi a ranar da daddare. Wani irin k’ululu ne y’a tsaya min a mak’ogaro na kasa furta komai sai binta nake da ido. Har sai da ta gaji da kallon ta bushe min ido tana furta “AYSHA lafiya? Kika shiga irin wannan shock haka?” Na saki ajiyar zuciya mai k’arfin gaske kafin na fashe da kuka na ce “Abu dhabi fa kika ce Anty Khadi? Wallahi bana son mutumin nan kuma duk da haka ba zai barni cikin y’an uwana ba sai ya cilla ni wata uwa duniya.” Anty Khadi ta dafa cinyata ta ce “Ki saka a ranki wannan k’addarar ki ce, shi a can yake kasuwancin sa, baya ga haka kuma ya amince za ki karatun da kike so a can, ba shikkenan ba burinki da na Maminki ya cika kun samu Wanda zia barki ki yi karatu.” Kuka nake sosai a jikinta na ce “Ni na hak’ura da karatun har abada in dai don haka aka d’aura min aure da shi.” Aunty Khadi ta ce “Aa fa AYSHA, yanzu ai lokaci ai ya k’ure ko so kike a fara k’irga Miki aure? Dukkan wasu shirye shirye sun kankama yau za ki bi mijinki.” Daga haka ta mik’e rik’e da d’an jaririnta sunan Abba muna ce masa Jawad ta fice. Kifewa na yi akan gado. Kukan ma da nake yi y’a d’auke d’if ba abinda nake ji a zuciyata sai wani irin matsanancin b’acin rai da tashin hankali Mara misali. Ban san wainar da ake toyawa a cikin gidan ba, don ban tashi ba sai daf da magriba, cikin matsanancin b’acin rai da na k’uncin zuciya. Na ma manta da zancen wai yau Mijina zai tafi da ni Abu Dhabi. Wanka kawai na shiga ko na ji sanyi a raina. Ina fitowa d’aure da towel a jikina na ga gari ya yi duhu. Sai ji na yi an turo k’ofa an shigo ina d’aga kai na ga Anty Khadija rik’e da wani k’aramin akwati a hannunta tana kallo na da alamun rashin wasa a fuskarta ta ajiye Box d’in ta ce “Ashe ma kin yi wanka, don har ya fara waya jirginku k’arfe goma zai tashi kada a yi delay. Ki samu ki shirya ga can k’anne ki suna jira ku yi sallama kafin a kai su d’akin mazajensu.” Wani irin rawa jikina yake ina kallon Anty Khadija da sam abinda take fa’da baya damunta naga itama yau har da kishiya za’a kai mata amma sam bata damu ba, mace ce mai wata irin zuciya Mara misali. Ta fita sai gata ta sake dawowa wannan karan kaskon turaren wuta ne a hannunta sai zabga k’amshi yake ta ajiye daf da ni. Sannan ta mik’a min Humar da kwalacca tana danna wayarta ta k’ara min a kunne “Maminki zata Miki magana, saura ki mata kuka ki d’aga mata hankali.” Ai kuwa ban ji kashedin Anty Khadija ba ina karb’a na fasa mata kukan sosai. Kamar ba zata yi magana ba, sai can ta saki ajiyar zuciya ta ce “Yi shiru Babyn Mami, ki kwantar da hankalinki zan Miki wani alk’awari muddin kika yarda kika yi zaman aure da kyau cikin soyayya da kulawa ni kuma zan share Miki hawayenki zan kuma dawo gidanku.” Na bu’de ido na da sauri Har ban san sanda murmushi ya sub’uce min ba na furta “Da gaske Mami?” Sautin murmushi ta na ji tana furta “Am serious Baby, buri na kawai ki bawa Mara d’a kunya.” Haka ta min nasiha sosai sannan ta ce “A cikin akwatin da na aiko Miki da kayan da zaki saka yau, akwai magunguna a ciki kada ki yi wasa da su masu kyau ne na gaske na saka matar ta rubuta Miki duk bayanin yarda zaki amfani da su. Allah ya miki albarka ya yiwa rayuwar aurenku albarka ki dage da biyayya AYSHA ko kya rabauta duniya da lahira.” Daga haka ta yanke kiran ina ta fa’din Hello Hello Mami na, amma ban ji ta ba. Hakan yasa na sauke wayar daga kunnena cikin mutuwar jiki da ta zuciya wasu hawaye masu zafin gaske suka shiga zubo min. Wa zan yiwa soyayyar? Wa zan nunawa kulawar? Wa zan wa biyayyar? Wata zuciyar ta amsa min da MAMUDA MAI KATON CIKI. Sai kawai na lumshe ido na ina sake hasasho shi a cikin duhun idona hankalina y’a sake tashi, gani nake ko da wasa ma ba zan iya d’aukar nauyin wannan mutumin ba. Anty Khadi na tsaye tana kallona Har ta gaji ta mik’a min kwalaccar haka kawai sai naji k’arfin zuciya yazo min don zuciyar ce ta bani shawarar na je gidan Mamudan Amma zallar rashin kirki da zan dinga nuna masa sai ya gaji ya sake ni, kuma ba zan tab’a yarda ya kusanceni ba, sai me don an k’irga min aure ai ba kaina farau ba. Haka na shirya sai dai ban saka komai a fuskata ba. Laffayar ma da take ta zuba wani cool k’amshi Anty Khadija ce ta na’da min. Ta ja hannuna muka fita parlorn gidan inda sauran y’an matan Abba da za’a kai Gidajensu suke. Kallonsu Kawai nake d’aya bayan d’aya don zuciyata ma ta bushe na kasa kukan sai wani irin tafasa take hakan yasa nake fesar da huci a kai a kai. Hucin da yake bayyana Har a k’ofofin hanci na. Dangin Ustaz ne suka fara zuwa suka tafi da Humaira. Ta zo rungumeni na janye jikina ina jin haushin ta da tsanarta sosai a raina. Ina kallo sauran ma duk aka fice da su. Gidan ya yi tsit daga ni sai Umma sai Aunty Khadii da take zaune a gefena tana sake kwantar min da hankali. Ni dai ido kawai na Lumshe daidai lokacin Abba ya shigo shima ya k’araci nasiharsa ban bu’de idon ba. A k’arshe ya ce “Allah ya baki ikon sauke nauyin da Allah ya d’ora Miki.” A raina na ce “K’warai kuwa nauyi, ko da kanku kun san ni y’ar fucilata da ni wannan mutumin ya min nauyi, ba mamaki daga ranar da yazo karb’ar hakkinsa ya ragargaza ni na Mutu kowa ma ya huta. Na tuno first night d’in mu da Ustaz yarda na ci bak’ar azaba ina ga wannan mai randar cikin ga jajayen ido fici fici daga ganinsa ka ga jarababben mutum. Abba da kansa ya ja hannuna zuwa waje wajen Mamuda da aka ce ya zo. Haka na zama tamkar rak’umi da akala na kasa wani motsi zuciyata ta soye idanu na fes nake kallon mutane. Ban damu da barin gidan ba don su kansu mutanen gidan na saka musu alamar tambaya a kan su da k’yar idan sun damu da farin ciki na. Suna gaban motar shi da wancan abokin nasa ni kuma ina bayan Mota ni da Yaya Usman da yake ta faman aikin lallashi na. Sai dai ko gezau kallonsa kawai nake. Mamuda mai tulun na ji ya ce “Ka rabu da ita Usman, nan da gobe zaka ganta warai, ai ba a lallab’a bazawara tunda ta riga ta San da’din aure ita kanta na San yanzu a matse take mu ka’dai ce….” Abu na ji ya sake tokare ni a k’irji. Jin yarda yake kalamai kamar yazo daga k’auyen k’awai na yi shiru ina tunanin izaya iri iri da zan masa har sia ya gwammace bai San wata Aisha ba wallahi. Yaya Usman ya ja hannuna ya rik’e sanda za mu yi sallama a airport cikin wata irin murya ya ce “I mish you lil sis ne a good girl please AYSHA!” Sai a lokacin kuka yazo min na fa’da jikinsa ina sakin wani irin wahaltaccen kuka. Shima kukan yake kafin ta janye ni daga jikinsa Naga ya juya da sassarfa ya bar wajen da sauri. Na lumshe ido na, na yi kuma saurin goge hawayen don bana son Mai tulun ya ga lagona. Muna hawa jirgin na nemi mai tulun na rasa don ni ban sani ba ko ya shigo ko bai shigo ba. Haka kawai sai na dinga jin wani irin feeling a raina. Ga zuciyata ta na wani irin bugu kamar zata fito daga k’irjina. Na dai daure na zauna a kujerar da take daf da ni. Bayan tsawon mintuna guda sai ga wani mutum yazo yana nuna min boarding pass d’insa ya ce “Am sorry Madame, Seat d’ina ne.” Ban yi magana ba na mik’e na isa inda na ga kamar nan ne nawa. Wani mutum ne cikin wasu irin k’ananan kaya masu masifar kyau. Kansa sanye da p.cap ya rufe fuskarta sa bayansa jingine da kujerar jirgin kamar mai barci. Na d’an bi shi da kallo kafin na tab’e baki na zauna. Sai zabga k’amshi yake kunnensa kuwa headphone ne a mak’ale. Zama na ke da wuya aka fara sanar da tashin jirgin. Hakan yasa gaba na y’a dinga fa’duwa musamman ganin yarda jirgin yake kamar gargada. Ina kallo kowa ya fara fastening seat belt d’insa amma ni hannu na ma rawa yake don rabo na da jirgi tun ina k’arama. Ji na yi mutumin ya zura hannunsa kawai don saka min belt d’in a masife na ture hannun nasa cikin bala’i na ce “Mahaukaci ne kai ko na ce maka ina da buk’ata?” Hannu ya saka ya d’auke p.cap d’in fuskarsa wata irin fa’duwar gaba ce ta same ni ganin Wanda nake zaune a kusa da shi…… 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….59 NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Zuciyata idan banda matsanancin bugu ba abinda take yi. Na dinga ganin wani irin bak’in duhu a idona. Ji na da gani na ya d’auke d’if. Bayan nan ban sake sanin inda nake ba sai farkawa na yi na ganni a gadon asibiti. Na bu’de idona da suka min nauyi sosai na tarar da jama’a birjik a cikin faffad’an d’akin asibitin. Dukkansu attention d’insu na ga ya dawo kai na. Umma ta k’araso bakin gadon da sauri. Tana kama hannuna cike da kulawa ta ce “AYSHA, me damunki?” Lumshe ido na na yi kafin na dafe kaina da yake min matsanancin ciwo. Fuskar wancan mutumin kawai nake gani a idona. Tunda na fara girma na d’orawa kaina son auren kyakykyawan namiji ashe ba zan samu ba. Ko kuma Allah ne zai nuna k’udirar sa a kaina ta hanyar hukuntani da laifin tozarta Ustaz. Allah na tuba na fa’da Wanda furucin iya busassun leb’ena suka tsaya. Sake kwatantoshi da ganin surar sa a zuciyata nake. Mummuna ne sosai wallahi irin munin da kana gani zaka furta kai tsaye. Ban da munin yana da k’aton baki, k’aton ciki. Sai dai daga ganinsa ka San Naira ta zauna daga yarda ya baza babbar rigar shadda mai tsada. Ga k’amshin turare yana ta bazawa. Kana ganinsa kaga irin mutanen nan da suka yiwa ku’di taka haye ba asalin wa’danda suka gada ba. Hawaye ne kawai y’a fara zuba daga kwarmin ido na. Umma na ji tana Shafa min kai daidai lokacin da Abba ya ce “Humaira taje ta kira Doctor maza ta sanar masa na dawo hayyacina.” Ba’a d’au lokaci ba Doctorn ya shigo a d’an hanzarce yana duba na yana Zare robar da take Sadar da ruwa cikin jijiyata. Ya kalleni cike da kulawa ya ce “Yanzu me ke damunki?” Muryata a dashe na ce “Ba komai.” Don kuwa ni kaina na zance ga abinda yake damuna ba gwara kawai na ce masa bakomai d’in don bashi da maganin damuwata. Ina kallo ya jinjina kai yana kallon Abba ya ce “A kula sosai, Alhaji don idan ba haka ba akwai yiwuwar ta iya samun hawan jini. Don a yanzu ma Allah ne ya kiyaye Allah ya bata lafiya. Zamu rik’eta anan for 2 days zuwa abinda ya yi hali, don muga yanayin jikin nata da abinda yake damunta.” Abba d’aga kai kawai ina kallon yarda yake komai a sanyaye. Daga haka likitan ya fice yana sake rok’on a barni na huta sosai kada a dameni da hayaniya. Daidai lokacin mayataccen k’amshin Ustaz ya cika Ilahirin d’akin Asibitin. Ina kallo AYSHA ta mik’e tana furta “Ustaz ya zo Umma, ga k’amshinsa nan.” Na runtse idona da sauri takaicin Humaira yana sake nakasta wani sashe na zuciyata wato itama ta San k’amshinsa kenan. Ina jin sallamarsa cikin Husky Voice d’insa da take bayyana zamowarsa jarumin namiji. Da sauri na runtse ido na. Don bana son a fahimci cewa ba barci nake ba. Bayan ya gaishe da su Abba. Ina jin takunsa zuwa bakin gadon da nake, yarda yake taku haka zuciyata take bugu da k’arfin gaske. Ya d’an tsaya kafin ya ce “Abba ai barci take bata farka ba.” Abba ya ce “Ta farka fa Ahmad, sai dai idan sake komawa ta yi.” Humaira ce ta k’araso don ta k’asan ido na nake hango tahowarta, ina kallon kuma yarda Ystaz ya bata duk attension d’insa da kulawarsa. Wani irin hawaye na ji ya zubo min a gefen ido na. Ina ji ta ce “Lah, Abba mafarkin kuka ta ke yi.” Abba ya ce “Wani irin mafarkin kuka kuma Humaira ke me yasa baki da kai ne. Matsa na gani.” Abba ya saka hannu y’a shafi hawayen gefen ido na yana furta “Tabbas, da gaskiyarki Humaira sai dai mafarkin kuka take ba, zahiri ne kukan take. Wato AYSHA kina jin abinda Likita ya ce ko? Ba zaki cire damuwa daga ranki ba ko? To wai ma me aka Miki da y’a tsunduma ki a wannan halin? Na ga dai duk abinda kike so shi muke yi Miki.” Humaira ce ta ce “Abba ka mata a hankali, ba mamaki wancan abinda aka mata ne Har yanzu bai bar ranta ba. A hankali komai zai wuce. Abba ya ce “To abinda ya riga ya wuce ba ya wuce ba, meye na dawo da abu baya. Allah ya mana magani shi yasa fa nake ta lallab’ata gidan Ahmad ma ban tilasta mata komawarsa ba.” Gaba d’aya jin magangansu nake suna k’ara harzuk’a zuciya ta. Na mik’e da sauri fuskata a tsuke na mayar da gashina da ya kwanto saman fuskata. Ustaz yana gefe ya zubo min ido ni kuwa wata harara na zuba masa. Madadin na ga b’acin rai a tare da shi, sai naga ya saki murmushi ya ce “Aysha, ya jikin?” ban ko amsa ba na shige toilet duk da ban san me zan yi a ciki ba. Amma har ga Allah kawai su d’in ne bana son gani gaba d’ayansu har su Abban. Ina shiga toilet na saki kuka a hankali. Irin kukan nan me cin rai. Ba na so su ji muryata don haka na toshe bakina da d’ankwalina. Don har abada na daina nuna musu karayata. Tsawon lokaci ina cikin toilet d’in da ban san me nake ba banda kuka. Har sai da na ji ana buga min toilet Umma tana kiran suna na. Hakan yasa na watsa ruwa a fuskata na goge fuskar don bana son a ga alamun na yi kuka. “Fito AYSHA ga mijinki ya zo.” Shine abinda na ji Umma ta fa’da wani irin tarnak’in b’acin rai na ji a zuciyata. Da wani irin k’arfin hali na murza lock d’in k’ofar na fito fuskata ba yabo ba fallasa. A tsaye na ganshi da k’aton cikinsa wayoyinsa manya a hannunsa. Gefensa kuma abokinsa ne me irin kamanninsa. So nake na danne abinda yake raina don na nunawa Ustaz hundred percent na amshi Mijina da hannu bibbiyu. Sai dai gabban jikina Sun k’i bani ha’din kai musamman idona da ya sake kawo ruwan hawaye, da gaske ko ganin mutumin bana son yi. Tuni hawaye suka fara zubo min batun bawa Ustaz mamaki ya kau. Na zauna a gefen gadon ina share ido na da handkerchief d’in da yake hannuna. Ina kallo Ustaz ya mik’awa mutumin hannu suka yi musabiha. Ustaz d’in Naga ya kalleni sai kawai ya tab’e baki ya saka kai ya fice daga d’akin. Abin haushin haka duk mutanen d’akin suka dinga ficewa da sauri kamar ha’din baki. Mutumin da ko sunansa ban sani ba ya kalleni ya ce “Amaryata, ku gaisa da babban abokina mana.” “Amaryar Ubanka…” Haka naso na furta a zahiri sai dai na kasa, sai ha’diye wani irin yawu mai d’aci nake. Na tsuke fuskata ban kuma gaishe shi ba, ji nake kamar na kashe shi ko na daina ganinsa balle har ya kira ni da amaryarsa mutum kamar wani basamude. “Ku gaisa mana.” Ya fa’da da y’an muryar hassala hakan yasa na d’ago na zabga masa harara. Sai na ji abokin nasa ya ce “Ka mata a hankali Mamuda, ai yarinya ce sai ka bi da ita a hankali kafin ku saba.” Duk maganar duniya da suka yi na k’i amsa musu ko guda ina ji gajiya suka yi suka mik’e suka min sallama ha’de da ajiye min bandir d’in dubu guda biyu. Na bi bayansu da kallo duk a maganganunsu ba Wanda ya min ciwo kamar cewar da suka yi wai matarsa ce ta Mutu a haihuwar d’ansu na biyar wato ma zuwa zan yi rainon yara. Kasa jurewa na yi na saka kuka sosai. Wannan karan ban toshe baki na ba don ban k’i kowa ma ya ji ba sai me? Gwara ma su sani Da gaske ba zan auri wannan abin ba. Kwana biyun da na yi a asibiti na yi su ne cikin wani yanayi da zan iya kira na ciwon zuciya. Hakan kuma ya kasa b’oyuwa gareni. Ni ka’dai na San zafin da nake ji a zuciyata. A haka dai likita ya tattara ya sallame ni don ana shirin fara biki jibi. Bikin da naji suna cewa wai har da d’aurin aure na da tariya ta za’a ha’da, wai mijin zai wuce da ni Abu Dhabi. Inda a can yake gudanar da dukka harkokinsa. Ba irin abinda ban kissima a raina ba na son gujewa auren mutumin nan sai dai duk inda na b’ulla sai naga hanyar ba mai b’ullewa ba ce. Ranar da aka sallame ni ko na ce Abba ya nemi sallama ina shiga bedroom d’ina Humaira ta shigo a guje ta fa’da jikina tana furta “Oyoyo My sisi an sallamoki ashe? Bari na kira Ustazu na na gaya masa….” Wata Uwar harara na watsa mata a kufule na ce “Ke bana son munafunci ki kira shi ya min Uban me?” Ta marairaice ta ce “Shi fa ya ce idan an sallamoki daga asibiti na kira shi ku gaisa.” Na ce “Ni kuma na ce bana buk’ata, Humaira ki shiga taitayinki. Ki kuma fice min a d’aki bana son hayaniya idan ba haka ba daga ke Har Ahmad d’in wallahi zan ci muku mutunci.” Ta wani irin waro ido ta ce “Ustazun?” Na ce “Ko Ubansa ne, Munafukan banza kawai.” Na kuwa shiga zuba masifa kamar zan ci Babu. Ina kallo ta fita daga d’akin jikinta a sanyaye. Na bi bayanta da harara da kallon jin haushi. Bata wani da’de ba sai na ji an turo k’ofa. Umma ce fuskarta a ha’de take kallona ta ce “ AYSHA me ke faruwa ne? Humaira ta je min da wani banzan zance, wai ta lura kina son mijinki don haka ita ta fasa aurensa, da gaske ne abinda ta fa’da?” Kamar zan k’aryata Humaira sai dai ina ga wannan ce gab’ar da ta dace na gayawa Umma abinda ke damuna a hankali na furta “Eeh Ina son sa Umma.” Wani irin zabura na ga Umma ta yi ta ce “Kina son sa fa kika ce AYSHA? Wani irin zance ne wannan? Gobe fa za’a kawo lefe kuma goben ne kamu ta ya kike son na je na sanar da jama’a an fasa da Humaira ke za’a mayar d’akin Mijinki, kamar fa hakan bai dace ba Aysha mu yi ta yin abu kamar wasu k’ananan mutane, mutumin da yake son ki Har fa an karb’i sadakinsa, shikkenan kullum a aurenki ke sai an samu irin wannan matsalar? 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA 61. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. UBANGIJI ALLAH YA JI KAN AHMAD ISA KOKO MAI KARATU NA RAI DANGIN GORO, ALLAH YA GAFARTA MASA YA SANYAYA MAKWANCINSA DA IYAYENMU BAKI DAYA. Cab’ ko kun san wa na gani? Da sauri na sake ware ido na don son na gasgata abinda idanun nawa suka nuna min. Amma still shi d’in ne dai yana sakar min murmushi idanunsa na wani kalar lumshewa. Sanye cikin kayan da suka masa bala’in kyau maroum shirt da wando black. Saman kansa kuma p.cap ce. Dole zan kasa gane shi don ban saba ganinsa da irin kayan ba. Sun masa masifar kyau. Ya gyara zamansa sosai yana facing d’ina ya ce “Ba mafarki kike ba, ni ne dai Ustazunki.” Wani irin sanyi na ji yana shiga duka sassan jikina, bak’in cikin da ya cunkushe a zuciyata ya dinga yayewa da ka’dan ka’dan. Hankalina ne ya dawo jikina tunanin ko dai suna tare da Humaira tunda da idona naga sanda danginsa suka zo d’aukarta. Don haka murna ta ta koma ciki na ce masa “Ina Humaira? Kuma tafiyar za ku yi? “ Ban ji ya min magana ba sai kusanto da jikinsa da ya yi daf da nawa na ji ya manna min wani irin deep kiss a baki. A hankali ya zare jikinsa yana lumshe ido ya mayar da kansa baya cikin husky voice ya ce “You get your answer right?” Wannan ka’dai ya isa ya tabbatar min Ustazu na ya dawo gare ni tunda na San ba zai tab’a aikata hakan gareni ba sai da k’wakwkwarar hujjar zamowata halaliyarsa. To ya aka yi haka ta faru? Shine abinda yake min kai kawo a zuciyata. Sai dai farin cikin da nake ciki ya danne tasirin tambayar tawa. Ganin yarda na saki ido da baki kamar wawuya yasa Ustaz ya bu’de lumsassun idanunsa na ga ya jawo hannuna ya ce “Ko still baki yarda ba? Humaira na gidan Mijinta ni Mijin AYSHA ne.” Ya fa’da yana nutsar da idanunsa cikin nawa. Hakan da ya haifar da wani lamari mai girma cikin zuciyata, wasu irin abubuwa suka dinga min yawo a sassan jikina. Na lumshe ido kawai bayan Ustaz ya saka kai na a gefen shoulder d’insa a kunne ya ra’da min. “Na san kina son jin komai but for now ba abinda zan ce Miki is a long story ki yi barci na San kwana biyu ba kya samun barci kina kukan Humaira ta k’wace Miki Miji ko?” Ban ji kunya ba na d’aga kai ina sakin murmushi Ustaz y’a danna clip d’ina da yake hab’ata ya furta “Ana so ana kaiwa kasuwa..” murmushin na sake yi don bani da bakin da zan bu’di ido na k’aryata shi. Na lumshe idona kawai ina hango mu a wata duniya mai girman gaske, na kasa barcin zallar soyayyar Ustaz da Muradinsa ne kawai a cikin zuciyata. Ina sake kuma jaddada godiya ta ga Allah da ya sake mallaka min shi a karo na uku bayan na cire rai da samunsa. Ko ina Mamuda mai tulun? A zaton Ustaz barci nake don haka bai tashe ni ba, ni kuwa bakam na yi ina shak’ar k’amshin jikinsa cikin wani irin yanayi. Sam bana son ko kwakwkwaran motsi na yi don kada gangar jikina ta nesanta da shi. Sosai na shige jikinsa nasa shi kuma ya saka hannu cikin rigata yana Shafa baya na a hankali. Ban san sanda barci ya d’auke mu ba daga ni Har shi. Sai Asubar can k’asar muka isa. Gaba d’aya Ustaz ya rik’eni gam a jikinsa kamar wani zai k’wace ni. Ba mu sha wuya sosai da yake tun A Nigeria aka masa booking na hotel da komai da komai. A 5star Hotel muka sauka da yake garin na Dubai. Zuciyata fari k’al nake mayar da k’afata duk inda Ystaz ya saka tasa. Shima kuma bai yarda ya yi nesa da ni ba yana mak’ale da ni sosai a jikinsa Har muka isa D’akin da muka sauka. Bedroom ne da parlor da fa’dar k’ayatuwarsu ma b’ata baki ne, wani irin cool k’amshi suke fitarwa. Gadon ya sha gyara na musamman. Gani na yi kawai Ustaz ya fa’da toilet bayan mintuna ka’dan ya fito sanye da bathrobe hannunsa da towel yana goge jikinsa. A gaba na ya tsaya hakan yasa na yi saurin runtse ido saboda har yau ina jin kunyarsa musamman ha’duwa guda muka yi muka sake rabuwa. Hannu ya mik’o min bayan ya zauna a gefen gadon ya yi matashi da pillow idonsa a lumshe ya ce “Ki je ki yi wanka.” Ai da sauri na shige toilet don kunyar ganinsa nake a haka. Wankan na yi sosai kafin nima na ziro rigar wankan na fito daga toilet d’in. Yana nan a yarda na barshi stiil idanunsa a lumshe. A takura na tsaya a jikin bango shi kuwa a hankali ya bu’de lumsassun idanunsa yana kallona ya mik’o min hannu cikin wata irin yanayin murya ya ce “Come closer K’alb, Ki zo na nuna Miki yarda komai na jikina ya yi missing naki.” Nok’e kafa’da na yi ga rawar sanyi ina ji saboda a.cn da take d’akin kaina kuma na jik’o shi. Ya sake mik’o min hannu amma na nok’e kai, k’arshe ma sunkuyar da kai na yi. “Me kenan AYSHA ki zo na ce, kada ki bari na iso nan fa.” Ya fa’da cikin wata irin galabaitattiyar murya. Da sauri na juya baya ganin ya mik’e da nufin isowa inda nake na ce “Ka bari mana na saka kaya.” Bai bari d’in ba don ji na yi gaba d’aya ya d’aga ni sama shagwa’be fuska na yi na furta “Ni bana so, ka bari mana.” Ya ajiye ni a saman gadon kafin ya fara ware rigar jikina yana furta “Ni kuma ina so shine Amma abinda na fi so a kan komai a rayuwar nan. Ina son jikinki AYSHA da duk abinda yake tattare da jikin, ki bari yau ina nuna Miki wata irin soyayya fiye da ta first night d’inmu da ba mu yi ta cikin nutsuwa ba pls K’alb kada ki disashe farin cikin mu….” Wasu irin abubuwa da y’a dinga min ne yasa na yi gum da bakina don bama zan iya magana ba, lamarin ya girmi tunani na. Abu guda na sani Ustaz ya rasa dukkan nutsuwarsa a wannan daren. K’arshe kuka na saka masa don wahalar ta yi wahala. Ya jani jikinsa yana sakin wahalallen numfashi ya furta “Am sorry K’alb, yau ba ranar kuka ba ce ranar farin ciki ce da zata zame mana ranar tunawa every year, kin shayar da ni wani irin farin ciki mai wuyar fasaltawa. Ina rok’on Ubangiji yasa ki zame min mata har Aljanna yasa ki zama shugaban hurul ain… Allah ya sakawa iyayenki da alheri har ma da Mamin mu.” Lumshe ido kawai ina jin wani farin ciki na sake rub’anya a zuciyata. A ranar kam Naga wani irin tattali da gata da ban san akwai sa ba ma a duniya. Tabbas auren mutumin da kake so yake matsanancin sonka ni’ima ce da Babu ta biyunta a duniya. Wayewar gari a Abu Dhabi. Mun yi tane cikin wani irin farin ciki da tarin annashuwa. Fuskokinmu kawai zaka kalla ka San duk wata soyayya da jin da’di mun same ta a tattare da junanmu. Murmushi kawai muke aikawa junanmu. Ustaz ya kasa nesanta kansa da ni ina mik’ewa zai ja ni jikinsa ya ce “Honey moon muka zo Hajiyata, don haka sai abinda ya turewa Buzu na’di.” Ban hana shi ba, don na San hakan kawai zan yi mu samu shak’uwa ta dindin a tsakaninmu. Burina na goge masa hadda na cire masa tunanin kowace mace a ransa. Na dasa masa k’aunata mai zafi ta yarda koda sunan sha’awa ba zai sake kallon wata mace ba balle soyayya. Yanzu ma zaune nake a cinyarsa ina aikin murza gemunsa shi kuma idonsa a lumshe. Na ce “Ka fa’da min Ustaz yarda aka yi a karo na uku aka sake d’aura min aure da kai?” Idonsa ya lumshe yana murmushi bayan ya ha’da goshina da nasa ya ce “Ko Karen hauka ne ya cije ni dama ba zan sake ki ba AYSHA, ke ce wayonki ya kasa nuna miki wasa ake da hankalinki…. Kowa gudun b’acin ranki yake shi yasa Abba ya ce mu biyo Miki ta wannan hanyar a gwada a gani ko kina so na, idan har baki damu ba da niyyar auren Humaira da na yi to tabbas ba kya so na, sai muka ga kuma sab’anin haka. AYSHA ta shiga tashin hankali marar misali. Ba abinda ya fi bani dariya halin da kika shiga da kika ga Mamuda a matsayin mijin da zaki aura ranar ni da Humaira sai da cikinmu ya kusa k’ullewa don dariya.” Turo bakina na yi duk da nima abin yana bani dariya sai dai yanayin yarda suka dinga tunzira ni sai na ji zuciyata ta hasala na saka masa kuka. Ja na ya yi jikinsa yana furta “Easy mana madam, tsokanarki nake, ki bari na baki labarin yarda komai ya canja mana.” Na lumshe ido na ina rungume a jikinsa ya fara bani labari. Tun sanda court ta wanke ki daga zargin da take miki, da na hango irin kallon tsanar da kike min sai da k’irjina ya buga. Don na San tabbas kallo ne da yake nuni da sai na rama duk abinda ka min. Ban sake tashin hankali na ba sai da Naga kin min kallon ‘d’iban karan mahaukaciya k’in watsar kina tauna leb’enki cike da tsiwa. Ban sake sarewa da lamarin ba sai da na biki gida nan ma na ga Babu wata mafita don kin k’i saurarata. Haka na koma gida gwiwata a sanyaye. Mommy na gani a parlor don haka da sauri na zube a kujerar da take kusa da ita. Ta dubeni cike da tausayawa don tun afkuwar lamarin ina hango tsananin tausayi na a idanunta, musamman ganin bana cin abinci bana walwala sam. Lawyoyi iri iri na nema k’wararru don su saka hannu a shari’ar Amma suka ce ba ruwansu ba zasu iya wannan shari’ar mai sark’ak’iya ba. Tunda lamari ne na manyan k’asa minister da kansa babu wanda kuma bai San shi wajen tsaurin rai ba, yana iya sawa a kashe mutum kuma ba abinda za’a yi. Mommy ta dubeni cike da tausayi ta ce “Yayansu ya shari’ar ta kasance?” Murya ta a dashe na ce “Ta yi Free Mommy, sam bata da hannu a duka wannan abubuwan daga wannan Har wancan wata ce can daban mai kama da ita, da ake zaton twins ne.” Mommy ta waro ido tana furta “Are you serious Yayan su? Idan kuwa haka ne da wani ido zan dubi yarinyar nan? Hasbunallah!” Na ja ajiyar zuciya na ce “Ba ke ba ma Mommy, ni kaina kallon tsanata nake gani muraran a idanunta, Ban ga kuma laifinta ba, tunda a sanda abin y’a faru kowa ya kasa mata uziri.” Mommy ta ce “In sha Allah zata zama mai halacci a gareka ba zata juya maka baya ba Yayansu, amma ni kam bani da bakin da zan tareta na nemi afuwarta kunya ma ba zata bar ni ba.” Wannan dalilin ne yasa har yanzu baki ga Mama tazo ta miki magana ba. Haka na dinga zaryar zuwa wajenki kina k’in fitowa har Usman ya bani shawarar na rabu da ke Har zuwa sanda zaki huce don kan ki. Don yanzu kam zuciyarki a zafafe take wajen son ganin kin yi ramuwar gayya. Na k’i bin shawarar Usman na dangana ga Abba. Shi ma exactly irin shawarar Usman ya ba ni. Hankalina ya sake tashi gani nake kamar na sake rasa ki Har abada. Don haka na dinga yiwa Abba Aiken manyan mutane Har Abba ya gaji ya bada shawarar yarda aka yi. Abba ya san ba takardar saki Na baki ba takarda ce kawai mai d’auke da kalaman soyayya. Ba kuma wani Humaira da zan auri Cousin d’ina ne ya ganta wqta rana ya raka ni wajenta ya mak’ale yana son aurenta don haka Abba ya b’ullo da wannan dabarar muka dinga wasa da hankalinki…” turo baki na yi alamar shagawab’a na ce “Shi kuma waye wannan mutumin?” Ustaz ya yi dariya sosai kafin ya ce Manager na ne na companyn shinkafa duk muka shigo da shi don a sake b’atar da hankalinki. Ban tabbatar kina so na ba sai da Naga yarda hankalinki ya tashi akan an ce Miki Humaira zan aura. Ba Wanda baki bawa dariya ba a parlorn ganin yarda taurin kan ki zai saka ki rasa abinda kike so, saboda miskilanci. Duk abinda kike yi sau tari Humaira tana min vedio ta tura min, na dariya na yi dariya na tausayinki na tausaya miki. Yanayin da kika shiga a asibiti da kika ga Mamuda shine abinda yafi bani dariya ina kallon yarda kika dinga wurga masa kallon tsana zuciyarki na harbawa don ana gani ta k’irjinki yarda take harbawa da sauri sauri. Miskilanci da nurk’ufanci AYSHA bai yi ba ki rage kin ji K’alb?” Huci na furzar ina masa hararar wasa na ce “Amma Allah ya sani kun wahlar da ni iya wahalarwa kun kuma Bawa zuciyata matsananciyar wahala don ko barci gagara ta ya yi Allah ne ya yi da kwana na a gaba.” Ahmad ya mintsini kumatuna ya ce “Ba wanda ya ja miki sai miskilacin ki, yanzu alal misali ace wannan mutumin aka baki ya .za ki yi?” Na runtse ido na kafin na furta “Ba yarda zan yi, sai dai na San tabbas zaman aure da shi zai iya zamowa ajalina wallahi murus zan iya mutuwa.” Ustaz ya yi dariya ya ce “Na san yarda zuciyarki take son auren mai kyau don haka na ha’daki da shi, sai ga shi kin fa’di jarabawar warwas!” Na mik’e daga cinyarsa ina turo baki. Nazeefah★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….64. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. *Gagara gasar masu gasa, tsohuwa kuma fasihiyar marubuciyarku HABIBA ABUBAKAR IMAM IKARA ta sake yunkuro mu ku da wani shahararren littafin ta wanda babu nadama a cikin tafiyar, KUSANCI , littafin da zai zamo gagara tsara, littafin da ba'a taba zuwa da irin salonsa ba, tafiyar ta na da nisa mikakkiya ce wacce na ke son duk wani masoyin littafan Hausa da masoyin Yar Gidan Imam ya shigo ayi tafiyar da shi, ku yi sauri ku shigo gidan kusanci domin samun abinda zai tafi da dukkan damuwarku. Maza ku biya kudin karatunku domin morewa wannan labarin ta wannan asusun 2083086009 Habiba Abubakar Imam UBA BANK Naira 1000 daya ne kacal amma ga bonanza ga mutane dari da zasu fara biya zasu biya nera 500 ne kacal kafin ya koma asalin farashin sa sai ku yi tururuwa ku shigo domin ku ci garabasar bonanzar, za ku tura shaidar biya ga wannan lambar 08033484021 ko kuma 09069067488.* *Mun gode.* Ya hau girgiza kai yana furta “Ni ne zan Mutu AYSHA, ni ne kuma a cikin bala’i don bana jin zan iya kwatanta Adalci a tsakaninku, ina tsoron ranar k’iyama na tashi da shanyayyen b’arin jiki. Ba ki ji yarda zuciyata take bugu, ina tsoro AYSHA, Allah ne da kansa ya umarcemu da mu yi adalci tsakanin matanmu. Ya sanar da mu idan Har ba zamu iya ba to mu auri guda kacal. Abinda Har yanzu mazan yanzu suka kasa ganewa wallahi AYSHA ba a adalci, don haka maza da yawa zasu tashi da shanyayyen b’arin jiki. Ina cikin tsaka mai wuya AYSHA ban san menene mafita ba? Ya ya zan yi?” Ya fa’da yana runtse idonsa a hankali ya kai tafukan hannayensa saman k’uncina, kafin ya ware idon yana kallona hankalinsa a tashe. Idanunsa sun ka’da sun yi jajur da alama furucin nasa Har k’asan zuciyarsa gaskiyar maganar kenan. Ni kuwa kuka nake sosai kuka mai bayyana uk’uba da tsananin da zuciya ta take ciki. Kukan nake sosai shi kuma ya kasa rarrashi na ya dai zuba min ido har wayarsa ta fara ringing. Idanuna na kai kan wayar na ga an saka MY WIFE 2… da sauri na janye ido na daga kan wayar ina jin yarda zuciyata take fusga da k’arfin gaske. Numfashina yana shirin sark’ewa kai da gaske kishi bala’i ne musamman idan kana son mutum. Janye jikina na yi da sauri na fice daga d’akin. Ustaz bai biyo ni ba hakan yasa na shige nawa d’akin na zube a saman gado ina kokawa da numfashi na da na ji yana neman d’aukewa. Tsawon mintuna biyar na ji ya turo k’ofar d’akin. Ina jin sa ya zauna a gefen gado. Kafin ya saka hannu ya shafi fuskata “Ta shi K’alb, magana za mu yi.” Na bu’de idona a hankali ina kallon cikin idonsa da suka nuna galabaitar da zuciyarsa take ciki. Leb’ensa ya d’an fusga cikin kammalalliyar murya ya ce “Ki yi hak’uri tamu k’addarar kenan, ki min addu’a kuma Allah yasa na iya kwatanta adalci a tsakaninku ko da a fili ne, don na San a zuciya dai kam ba ni da iko da hakan. Zan tafi ga wata dattijuwa can Mommu ta aiko Miki da ita zata taya ki zama. Da ku’di da komai a drawer zuwa jibi da yamma zan dawo nan, amma gobe ma zan shigo mu gaisa, amma don Allah ki saka Hijabi idan na Miki waya zan shigo.” Wani yawu na ha’diye mai kaurin gaske. Wani abu na ji y’a cunkushe min a zuciyata. Ban san sanda na rik’e hannunsa ba ina murzawa da k’arfin gaske na saki kuka ina furta “Pls Ustaz kada ka tafi ka bar ni, wallahi zuciyata ba zata jure ba. Za ta iya failing.” “Ba zata yi ba AYSHA, ki daure ko wace mace da haka take sabawa. Ba a kanki aka fara kishiya ba, ki dinga tuna haka sai ki samu sauk’i a zuciyarki.” Ina kallo Ustaz ya janye hannunsa ya tafi da saurin gaske. Ban san sanda na runtse idona ba don tsananin kuka idona har yaji ya fara. Shikkenan Ustaz ya tafi wajen Hameeda zai mata abinda yake min, zai mata soyayya za su kwanta tare su yi wanka tare kamar yarda muke yi…” Na ji zuciyata ta buga da k’arfin gaske. Ni ce Har k’arfe ukun dare ina kwance a haka Sam na kasa runtsawa tun bayan da na je wajen Baba Atine wacce Mommy ta kawo min na bata abinci da wajen kwana, sai na dawo na yi kwanciyata cikin wani irin tunani mai wahalar da zuciya. Har a lokacin zuciyata Imagining Ustaz take a gadon barcin Hameeda suna romancing juna. Ban san sanda na furta kalmar “Na shiga uku” a fili ba. Yanzu haka zan yi rayuwar aure da Ahmad muna sharing d’insa da wata, haka kuma zan dinga ji a duk sanda Hameeda ta karb’i girki? Na dinga jin kamar zan Mutu. Anya zan iya kuwa? Na d’au wayata ina duba lokaci. Ganin k’arfe uku bai hana ni kiran Mami na ba. Tsawon lokaci tana ringing kafin Mami ta d’aga da alama ma barci take don muryarta ta bayyana hakan. “Baby lafiya? Kira a tsohon daren nan, Allah yasa dai lafiya.” Cikin shashshek’ar kuka na ce “Mami na, na kasa barci, zuciyata ciwo take ga kai na ya yi nauyi.” Mami a rud’e ta ce “Subhanallah, Shi Ustaz d’in yana ina? Kuka zauna baku tafi asibiti ba?” Na sake sakin kuka da k’arfin na ce “Mami ya tafi wajenta.” Cikin ki’dima Mamin ta ce “Ita wa?” Na sauke ajiyar zuciya na ce “Matarsa Hameeda.” Mami ta saki ajiyar zuciya ta ce “Wallahi Baby kin bani tsoro. Idan har na fuskanci matsalarki bakomai ke walagigi da ke ba sai kishi, Ya kamata kuwa ki ajiye shi a gefe, duk da an San yana da ciwo Amma yana zuwar wa mutum a inda ya d’auke shi. Idan ka d’auke shi da zafi zai zo maka da zafi, idan ka d’auke shi da sauk’i yazo maka da sauk’i. Don haka ina so ki dauke shi da sauk’i kamar yarda kika ga ni da Ummanku mun d’auke shi da sauk’i. Sai hakan ya zame mana alheri. Kada ki ba mu kunya.” Na runtse idona ina k’ok’arin sakawa kaina nutsuwa sai dai abin ya gagara na ce “Wallahi Mamina ba zan iya ba, kowacce mace da yarda Allah ya halittar mata nata kishin, ni Allah ya yi yo ni cikin mata masu tsananin kishi.” Cikin tsawa Mami ta ce “Za ki iya AYSHA, kowacce mace da kika gani koya ta yi kuma ta iya Har ta Saba. Don haka ba dalilin da zai saka ke kika sa iyawa, sai dai idan kin sakawa kanki son zuciya. Mata nawa aka yi wa kishiyar kuma suka zauna lafiya.” Fashewa na yi da kuka jin fa’dan da Mami take min madadin rarrashi. Hakan da ta ji ne ina ji ya saka ta tausasa harshenta ta ce “AYSHA, saurare ni, yi shiru haka, maza ki tashi ki je ki yi alwala ki yi sallah, za ki samu sauk’i a zuciyarki, kin ji? Maza tashi.” “To” na ce a sanyaye ina zame wayar daga kunne na na shige toilet. Cikin k’arfin hali na yi alwala kafin na fito na fuskanci alk’ibla na tada ik’ama. Ina sallah Ina hawaye ina rok’on Allah ya saka min nutsuwa a zuciyata ko na samo na tsallake wannan jarrabawar. Tabbas wallahi Babu maganin kishi a duniyar nan irin addu’a. Don na samu sauk’in zuciyata daga cikin kaso d’ari na b’acin rai na kaso talatin ya tafi. Sallahr da na yi na samu nutsuwa sosai sai ga shi barci ya d’auke ni mai nauyin gaske. Akwai magani sosai a cikin Sallahr dare maganin damuwa da b’acin rai da duk wani k’unci da aljihu da na zuciya. Allah ka bamu jumurin yin k’iyamallaili. K’arar waya ne y’a farkar da ni daga nauyayyen barcin da ya d’auke ni. Ina kai duba na kan wayar na ga an saka REALITY. Na d’an d’auke kai na ina kokawa da abinda na ji yana son dawo min. Ban d’aga wayar ba na ajiyeta a gefe na mik’e zuwa toilet. Cikakkiyar alwala na d’aura na fito na yi Sallahr asuba na koma na kwanta. Cikin barci na dinga jin hannayensa suna yawo a saman fuskata. Na bu’de idona da suka min nauyi a hankali ina zuba su a kansa. Tas da shi ya yi wanka ya yi wani fresh da alama ya yi kwanan nutsuwa ni ya barci cikin kwanan b’acin rai. Hakan yasa na mik’e fuskata a d’aure na shige toiket na banko k’ofar da k’arfin gaske Har da murza lock. Wanka na yi sosai na fito daga ni sai mitsitsin towel, dangwaliliya zan masa tunda har wani ce min yake na saka Hijab idan zai zo. Gashi na a baje yake sosai a saman wuya na. Har da y’ar wak’a ta na isa gaban dressing mirror na zauna. Ina kallo Ustaz yana ta sakin murmushi daga zaunen kafin ya kasa hak’uri ya mik’e ya iso inda nake zaune ina ta laila ya mai a cinyata. Zuro kansa ya yi ta baya na, yana goga hancinsa a wuyana yana shinshina a hankali ya ce “Baki missing d’ina ba ne K’alb, ina can duk kewarki ta dameni na rasa sukuni gashi ba dama na kira ki ina tare da Hameedah, amma gaba d’aya hankalina na kan ki. Idan na kira ki kuma zai zama kamar cin fuska ne…” ture shi na yi a jikina ina turo baki na. Don haushi ma maganar tasa ta bani. Wato sanar da ni yake tare suka kwana da matarsa kenan? Kamo hannuna ya yi ya manna ni da jikinsa ya rungume sosai. “Tsaya na samu nutsuwa AYSHA.” Da sauri na sake ture shi daga jikina ina furta “Ina ruwanka da ni, tunda kai ka yi kwanan farin ciki ni kuma na kwana da ciwon zuciya.” Murmushi kawai ya saki yana lotsa hannunsa cikin kumatu na ya furta “Kwantar da hankalinki K’alb, daga yau Ahmad ya zama naki ke ‘d’aya ba maganar sharing da wata. Ban baro gidan ba sai da na saki Hameeda, don bana son na cuceta ko na ci amanarta.” Na zaro ido don gulma na furta “Saki kuma? Why Ustaz?” Ya ‘d’aga min gira yana lumshe ido ya ce “Bana daga cikin mazan da zan iya adalci, ina kuma tsoron ha’duwata da Allah da shanyayyen b’arin jiki, shi yasa na zaunar da ita muka fahimci juna na bata dukiya mai yawa kafin na saketa, ina fatan hakan da na yi yasa ya zamo alheri gareta ta kuma fahimceni. Alhamdulillah kuma ta fahimceni kamar yarda iyayenta suka fahimceni haka Mommy ma tana fatan Allah yasa hakan ya zama alheri garemu baki d’aya. Amma fa na mallaka mata dukiya da kadara mai tarin yawa.” Lumshe ido na yi kawai wata dukiya da ya mallaka mata duk bata dameni ba. Wani irin sanyi na dinga ji a zuciyata sai dai haka kawai sai na ji sakin bai min da’di ba. Duk da dai ban sani ba. Da Azahar sai ga Mami na da Umma. Suka shigo fuskokinsu a ha’de. Da na ha’da ido da su sai da na ji fargaba tazo min don ban saba ganinsu a haka ba. Gaisuwata ma basu amsa ba suka fara min masifa fa’da suke sosai ta inda suke shiga bata nan suke fita ba. Cikin rawar harshe na furta “Ni fa ban san me na yi ba.” Mami ta wurgo min pillow tana furta “K’in ci gidanku AYSHA, kamar ya ba ki San me kika yi ba, saboda bak’in kishinki na banza kin saka an saki yarinya haka kawai.” Da sauri na waro ido na ce “Ni kuma? Wallahi ban san zancen ba, ba ruwana shi ya ce ba zai iya adalci ba ya saketa Wallahi ku tambaye shi ku ji.” Na fa’da hawaye yana zuba a idona. Ustaz ne ya zauna a gefensu bayan ya gaishesu ya shiga wanke ni tas a wajensu ya ce “Wallahi ba ruwanta Mami, ni ne da kaina na yanke wannan hukuncin.” Tsaf ya gaya musu dalilinsa sai na ga Sun saki ajiyar zuciya. Mami ta ce “Allah ya so ki, dama da da saka hannunki wallahi Mihammad ko Aliyu zan saka su zo su zaneki.” Daga haka suka mik’e suka tafi suna sake jaddadawa Ustaz sam bai kyauta ba, da ya aikata hakan. Duk da hakan da ya yi shi yake nuna shi mutum ne mai adalci. Shi dai shiru ya yi yana sosa kai. Muka raka su Har mota. Tun daga hanya Ustaz ya ja hannuna da sauri muka shige d’akinsa, ni da kaina a ranar na San ya yi missing d’ina. *****Ranar da muka yi sati biyu da dawowa Ustaz ya ce na shirya mu je ziyara gidanmu da gidansu. Gidansu muka fara zuwa nan na ga kulawa da soyayyar surika. Mommy mutuniyar kirki ce ashe, ta dinga ina ka saka ina ka ajiye da ni cikin mayalwaciyar fara’a. Haka ta tasa Ustaz a gaba ta dinga masa nasiha da ya kula da amanata da aka basa. Kada ta ji kada ta gani. Tabbas Momny mutuniyar kirki ce kamar surikar Nazeefa. Allah ya k’ara mata yawan rai baiwar Allah da bata damu duniya ba. Ta cika ni da abubuwan arziki muka tafi. Daga nan gidanmu muka je. A tsakar gida na tarar da su gaba d’ayansu Har Humaira da San bata rabo da zuwa gida. Na d’ane Mami na da sauri cikin murna ina furta “Mami k’iba fa ki ke yi? Ke da ba kya son k’iba.” Umma da take gefe ta ce “To Mara kai, ki kula da kyau kada ki kada ita… duk da ban so gaya miki ba.” Na waro ido ina kallon Mami da take ta rok’on Umma kada ta gaya min. Tana nuna Ustaz da yake tsaye yana d’an sakin murmushi. Da sauri na isa wajen Umma ina furta “Umma don Allah menene?” Umma na murmushi ta ce “Ai abin murna ne, gwara kawai a gaya mata na San sai ta fi kowa farin ciki, Mamin ki ta kusa samar miki k’ani.” Na wani irin waro ido kafin na daka tsalle…. A yi hak’uri kun ji ni kwana biyu shiru na d’an yi tafiya ne. Na gode masu bincikae Lafita ta. Jikar Nashe★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….62. NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Ina zaki?” ya fa’da yana cafko hannuna. Screen d’in wayarsa da ke ringing Na bi da kallo ganin an saka My wife tuni hankali na ya tashi, sai sannan zuciyata ta tuna min ba ni ka’dai nake da Ustaz ba ashe, wani kishi ya dunk’ule min a k’irji Har ina jin kamar ba zan iya numfashi ba. Cikin hanzari na janye jikina na fice daga d’akin da sauri, amma abin mamaki Ustaz ko sunana bai kira ba balle ya yi yunk’urin biyo ni. Ina ji yana kashe murya yana amsa wayar kamar Wanda yake waya da budurwa zafin k’irjina ya sake yawaita na fara tunanin haka zan cigaba da rayuwa da Ustaz muna sharing d’insa da wata. Tuni k’walla ta fara suntiri akan fuskata. Na zauna saman kujera na zuba uban tagumi kawai. Tsawon mintuna ya fito daga d’akin yana kiran “K’alb, ina kike ne?” Ban amsa masa ba don wani haushinsa ne na ji y’a cunkushe min a k’irji. Da zafin zuciya nake hararar inda yake tahowa. Cikin sanyin jiki ya zauna daf da ni, yana k’ok’arin ja na ni kuma ina turjewa, amma bai fasa abinda ya yi niyya ba. Gani nake yanzu haka duk abinda yake min haka itama yake mata don haka na kawar da kai na da sauri na ce “Bana so fa.” Ha’de goshinsa ya yi da nawa yana sakin ajiyar numfashi da take fita da wani irin k’amshin mouth wash mai da’din gaske. “Me aka miki?” Ya fa’da cikin wata irin voice da ta kusa tarwatsa min zuciya, Ban amsa ba sai sake mik’ewa da na yi da sauri na fice daga parlorn zuwa harabar gidan ta baya wacce take kitchen. Don ba zan jurewa abinda yake min ba, tsaf zan iya bada kai bori ya hau, ni kuma bana son ya ga lagona. A Garden d’in gidan mai wadatattun shuke shuke na zube ina haki ina kallon yanayin wajen da yake fitar da wani irin ni’imtaccen yanayi mai sanyaya zuciya. Ban san sanda na ja jikina na kwanta flat ina mayar da ajiyar zuciya ba, idanu na a lumshe. Ban san sanda ya zo wajen ba na dai ji shi kwance a jikina ya yi min rumfa da nasa jikin da yake fitar da wani irin k’amshi, bai bani k’ofa ko guda ba da zan iya k’watar kai na ba, duk da bai sakar min nauyinsa gaba d’aya ba Amma fa na ji a jikina, wani irin hot romance yake sakar min mai zafin gaske da yasa na manta da wancan b’acin ran da nake ciki. Waje ne mai ni’ima da kyau ga shi ba kowa a wajen don haka ya samu sake yake yi abinda yaga dama da jikin nawa ba inda bai lek’a ya lasa ya shinshina ba kafin ya koma gefe ya yi kwanciyar rigingine yana kallon sama ya jawo ni jikinsa sosai ban san ya aka yi na ganni a saman cikinsa ba yana furta “A ramawa kura aniyarta K’alb, kin bar ni sai ki’da na da rawa ta nake ni ka’dai, ni da ko kiss har yau ban tab’a amsa daga wajenki ba, don haka yau ina son na ga kalar taki soyayyar.” Kunya ce ta kama ni sosai na kasa aikata komai, shi kuma ya kama fuskata da duka hannayensa biyun muna daf da juna cikin husky voice ya ce “Oya na rufe ido I need a French kiss, ki zama Good House wife mana K’alb.” Idonsa a lumshe yake na dinga kallon Cutable lips d’insa masu tsananin sulb’i da taushi duk da kunyar da nake ji Ban san sanda na kai nawa lab’ban kan nasa ba, wani irin ajiyar zuciya na ji ya sauke a hankali daga nan kam abubuwa suka riki’de zuwa wani yanayi mai girman gaske mai tsayawa a zuciya da ba zan iya tab’a manta shi ba. Wani Moment ne da ni da shi muka aikata a sannan kowa ya san irin son da d’an uwansa yake masa ba ka’dan ba ne. Wani irin barci mai k’arfin gaske ne ya d’auke mu a y’ar harabar wajen da iska take ka’dawa ko ta ina. Bamu tashi farkawa ba sai daf da magriba Ni na fara tashi na Ware ido ina mamakin barci mai nauyin gasken da muka yi. Na mayar da kallona kan Ustaz da ya ja hannuna ya matse gam. Na Zare hannun ina Shafa fuskarsa a hankali. Lumsassun idanunsa ya bu’de yana furta “Sleep Aysha, ki kwanta barcin bai isheni ba.” Na girgiza masa kai ina furta “Lokacin sallah fa ya kusa.” Da sauri na ga ya d’an ware ido yana kallon sararin samaniya sai kuma ya mik’e da sauri yana gyara sumar kansa da ta burkice gaba d’aya. Idanunsa ya nutsar cikin nawa ya furta “Kin shayar da ni wata irin soyayya da tasa na ji kamar a Aljanna nake, please za ki k’aramin anjima, ashe haka ki ke?” Da sauri na mik’e na shige k’ofar da zata mayar da ni inda muke.” Ina ji y’a biyo ni da gudu yana dariya nima gudun na saka zuwa cikin bedroom sai dai kafin na rufe k’ofa ya saka hannunsa ya shigo hakan yasa na shige toilet da sauri. Na fara wankan dole bayan na gama wankan na ga toilet d’in bakomai sai wasu y’an towel k’ananu da ba yarda za’a yi su rufe ni. Na d’aura ina kallon kaina a mudubi da sauri na waro ido “CAB a haka zan fita ya gan ni?” Hakan yasa na d’an bu’de k’ofar a hankali na ce “Ustaz, pls ka bani Hijab zan fito.” Da wani irin zafin nama na ji ya turo k’ofar yana k’are min kallo ya ce “Wai ke me kike nufi? A haka ne ba za ki iya fitowa na gan ki ba? Baki san ya halatta na ganki ba komai tare da ke ba? To bari ki ga wankan ma sake shi za ki yi, kuma daga yau in dai ina nan sunna zamu dinga bi, wanka za mu dinga yi tare.” Kafin na yi aune ya wafce d’an ficilin towel d’in da ke jikina da azama na runtse ido ina furta “Haba Ustaz me kenan?” A kunne ya ra’da min “Sunna kenan AYSHA, koyi nake da Manzon Allah.” Wani irin abu da yake min ne yasa na yi shiru k’arshe cikin wata irin rawar murya ya furta “Komanki mai kyau ne AYSHA, Anya Son ki ba zai min illa ba K’Alb? Bana gajiya da komai na ki.” K’afata rawa ta fara yi na kuma kulle ido na gam, ban san sanda ya kai ni Bathtub. Wannan lamari girmansa ya girmama tabbas Allah da ya k’addara soyayya da aure ya kamata bayinsa su gode masa don idan Har ka dace da Wanda kake so yake sonka to ka gama ha’duwa da dukkan farin cikin rayuwa. Ustazu na ya gama narkar da zuciyata da wata irin soyayyarsa mai zafin gaske a zaman mu na sati biyu a Abudhabi, ya saka na zama Qualified a kan komai na iya komai na tattalin Miji na. Ba ma rabuwar da ta zarta ta minti buyar duk sai na ji duniyar b’ata min da’di. Wani yammaci ana gobe zamu tafi saudiyya Ustaz ya ce mu shirya mu je wani mall da ke kusa da hotel d’in mu. Tsaf na fito cikin wata rigar larabawa mai masifar kyau kalar peach mai ratsin black hakan yasa na rufe kai na da mayafi bak’i da yake rigar mai fa’din gaske ce kamar julbab, na saka black shade a idona. Sanda na fita don mu tafi wani irin flash na dinga ji Ustaz yana sakar min ko ta ina. Ni kuwa murmushi kawai nake, Har Ustaz d’in ya zagayo ya ta bayana ya manna ni da jikinsa ya dinga d’aukar mu hoto wasu da yawa yana Fecking kumatu na da yatsun sa da suke danna clips d’ina. Ba k’aramin kyau muka yi ba, kafin mu gama na ga ya Zare shade d’in fuskata ya ajiye yana furta “Kina fita a haka ai na shiga uku, kallonki za su yi ta yi kamar su lashe ki.” Na turo bakina ina furta “Glass d’in ma? Kai ma fa na ga ka saka kuma kai ma Har kwalliya ka yi da k’ananan kaya wai yaushe ka fara saka su?” Ya ja hancina yana furta “Lokacin da nake son na burge Ayshatu.” Na yi murmushi kawai ya sake gyara min mayafi na ya rufe gashin kai na ruf kafin ya saka bakinsa ya tsotse jambakin da na saka tas yana lumshe ido ya ce “Wannan haramiyar ordinary men ne, sai Mijin Ayshatu baki San yarda jambaki ke Miki kyau ba ko?” Murmushi kawai na yi ina jin farin cikin yarda yake kishi na, alamu ne na tsananin son da mutum ke maka. Hannuna ya rik’e yana furta “Anya zan iya rayuwa Babu ke? Kamar fa saboda ke ka’dai da ibada aka halicce ni, Har yau fa zuciyata ke guda take so.”. Na yi far da ido na na ce “Hameeda fa?” Dariya y’a guntse ya ja hannuna yana furta “Ba kyau maganar mutum idan ba ya nan, sarauniyar y’ar rigima.” A mall d’in kuwa sai wani nan nan yake da ni, yana ta zabga tsaki ganin yarda wani yake ta bi na da ido. A zafafe ya janye hannuna yana furta “Mu fita Aysha, Dire cart d’in kafin wancan mayen y’a cinye ki da ido.” Na ajiye ya ja hannuna muka fita da sauri. Ko a mota mitar da ya dinga yi kenan Har muka isa gida fa’di yake “Matsalar auren mace mai kyau kenan? Shegun banza idanunsu akan ku, to daga yau wallahi na haramta miki fita ba nik’ab ko ina za ki kuwa?” Na waro ido ina furta “Har biki Ustaz?” Yana huci ya ce “Har shi AYSHA.” Ganin yarda ya tunzira sai na ja baki na na tsuke ina dariya k’asa k’asa. Azaba gaskiya Usta zu na akwai kishi na masifa. Har dare bai fasa mita ba da jawa mutumin nan Allah ya isa har na gaji na manna baki na da nasa ina aika masa sak’o mai zafi da ya saka shi yin shirun dole. Ban k’yalesa ba sai da na mantar da shi duk wancan b’acin ran tas sannan na samu salama. Kashegari kuwa muka yi sallama da AbuDhabi zuwa k’asar Saudiya. Fuskata sanye da nik’ab da wani burgujejen julbab. Haka dai na hak’ura ya zan yi? Sanda muka isa madina wani irin sanyi na dinga ji a zuciya ta. Musamman gani na ga ni ga kabarin Manzon Allah. Ban san sanda na saka kuka ba. Haka ma a makka da muka je ka’aba. Shima kuka na dinga yi ina yiwa duka dangina addu’a. Sannan na tsananta addu’a akan Allah ya daidaita Abba da Mami su dawo da aurensu don shine abinda na fi so fiye da komai a yanzu. Ustaz siyayya yake jibgawa duk inda kuma yaga kayan baby siya yake, sai ya ce wai ya san nan da 8 months ya d’Au babynsa “Allah Ameen.” Na ke cewa a zuciyata don nima ina son na ga Baby amma ni nafi son namiji shi kuma Ustaz ya fi son mace. A gida kuwa babu Wanda ya nemeni, sai dai Ustaz ya dinga ce min Sun yi waya da wane yana gaishe ni.” Tab’e baki nake in ce “Shine basa nema na.” Ustaz ya yi k’asa da muryarsa yana furta “Sun San kina can kina karb’ar lamari mai girma wajen Ustazun ki ya za’a yi su neme ki Madam?” A yi hak’uri remain few pages mu k’ark’are In sha Allah. Nazeefah★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….63 NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Na turo bakina kawai don ni sai na ji abin ya bani haushi. Ustaz dai bai yi min magana ba ya ja bakin kawai ya mik’e ya fice daga bedroom d’in yana dariya k’asa k’asa. Kashegari Ustaz shi ka’dai y’a fita don a kwana biyun da suka gabata wani matsanancin zazzab’i nake fama da shi ga amai da jiri. Shi kansa Ustaz d’in ba inda yake zuwa sai masallachi. Ina zaune ni ka’dai na zuba tagumi da hannu bibbiyu ba abinda nake tunani sai yarda rayuwa ke juyin waina. Da yarda lamarin duniya ya zama abin tsoro. Tabbas na amince da cewa duniya ba matabbata ba ce. Babu komai a cikinta sai ru’dani. Rayuwar yanzu ta zama abar tsoro yau gareka gobe ga waninka. Duniya ta rikice masu ku’di kawai ke jin da’dinta yayinda talaka ke cikin wata irin rayuwa babu abinda ya dace ga bawa irin ya nemi kusanci ga Allah. Ya tsaya ya jajirce wajen bautar Ubangijinsa. Idan bawa ya yi hakan fak’at ya gama, sai ya tattara ya mik’a dukkan lamarinsa ga Allah ya yi addu’a Allah yasa ibadar da ya yi karb’abbiya ce. Saboda ba Wanda ya san ranar mutuwarsa Amma kam a wannan k’adamin da ake ciki sakankancewa ba ta bawa ba ce, wallahi duniya ta zo k’arshe. Kada ka manta da mak’asudin da ya saka aka halicceka don ka bauta wa Allah ne ba don ka shagala ba… wannan tunanin da na yi sai na ji hankalina ya tashi. Tsoro ya cika min zuciya ba tsoron komai ba sai na mahaliccina. Hawaye suka dinga ambaliya a idona. Na lumshe ido na kawai ina jin saukar su. Ban san sanda ya shigo d’akin ba sai ganinsa na yi durk’ushe a gaba na, ya dafe duka cinyoyina yana kallona cikin tashin hankali. Cikin wata irin murya ya ce “Me ya faru K’alb? Ko ciwon ne?” Na girgiza masa kai na. Ina k’ok’arin tsayar da hawayen ido na Amma na kasa. Ustaz bai fasa matsa min hannuna ba cikin sigar lallashi ya ce “Tashi mu je asibiti, da ina da iko da na mayar da wannan ciwon jiki na K’alb.” Kumatunsa na Shafa na ce “Ba ciwo ba ne Ustaz, tuno wa da tabbas za’a Mutu za’a ha’du da Allah shi ya d’aga min hankali, ina kuma tausayin Wanda bashi da shi a wannan halin da ake ciki na rashi a duniya mai ku’di ne kawai yake walawa.” Ustaz ya saki ajiyar zuciya, Ya lumshe idonsa ya ce “Da wannna tunanin nake kwana nake tashi AYSHA, kuma duk wani mai imani dole ne y’a dinga tuna mutuwa ha’duwa da Allah, da azabar kabari. Wallahi a duk sanda na tuna lahira na tuna akwai hisabi akwai wucewa ta kan sira’di na kan samu kaina da rasa duk wata nutsuwata, ina fatan Allah yasa mu dace. Wannan halin da mutane suke ciki kuwa bakomai ya dace garemu ba irin mu koma ga Allah mu nemi tuba da tsark’akakkiyar niyya mu k’udirce a ranmu tuba ne muka yi shi na Har abada ba zamu koma ga zunubi ba, idan muka aikata hakan tabbas zamu samu sauk’in wasu lamuran. Gaba d’aya jikin mu ya yi sanyi, ranar ko siyayyar da Ustaz ya yi ban duba ba. Haka muka zauna shiru sai da la’asar ta yi sannan muka tafi harami. Bama dawowa dama sai An yi sallah Isha’i. Amma yau yarda jikina ya matsa min a haramin yasa ba shiri Ustaz ya tattara ni zuwa asibiti. Dubawar farko da aka min, likita ya tabbatar da samuwar ciki a mahaifata na watanni biyu. Wata iri murna Ustaz ya dinga yi don Ban san sanda na ji ni a cikin jikinsa ba cikin tsananin farin ciki ya rungume ni. Yana furta “Alhamdulillah, bi ni’imatihi tatummussalihat..” ni kuwa murmushi kawai nake saki cikin matsananciyar jin kunyar likitan da duk Wanda yake wajen. Wai ni AYSHA ni ce da ciki na haihuwa a jiki na. Haka Ustaz ya ja hannuna cike da tausayawa muka fita zuwa harabar asibitin. Nan ma tsayar da ni ya yi a cikin hasken futilu ya saka duka tafukan hannayensa ya tallafi fuskata yana murmushi ya furta “Sorry K’alb, how I wish zan iya mayar da cikin nan jiki na da dukkan lalurar da yake saka ki. Amma ki saka a zuciyarki ibada kike. In sha Allahu za ki samu rabo mai girma a wajen Ubangiji.” Na lumshe idona kawai farin ciki yana sake cika min zuciyata. Da gaske na yi dacen Miji na bugawa a jarida na kerewa sa’a kuma. A hankali na furta “SHUKRAN LILLAH!” Sati guda muka k’ara jirginmu ya d’aga da mu zuwa Nigeria. Cikin walwala nake saukowa daga jirgin zuciyata cike da murna da zakwa’din ha’duwa da y’an uwana. Gaba d’aya ahalin Babanmu da na Baban su Ustaz suna tsaye a wajen jiran passenger. Wani irin farin ciki ne ya mamaye ni hango su da na yi Sun zo tarar mu. D’aya bayan ‘d’aya suka dinga rungumeni har Mommyn Su Ustaz. Ina jikin Ta na ji an ja hannuna ina juyawa na ga wata mata mai nik’ab ta rungumeni a jikina na San Mami na ce tun kafin ta bayyana kanta gare ni. Da sauri na d’age Nik’ab d’in ban san sanda na saki ihu ba na ce “Mami na!” Ta ce “AYSHA ta!” Na daka wani tsalle na ce “Allah yasa addu’a ta ce ta karb’u.” A hankali na ji Ystaz ya ce da Mami “Maminmu ta yi a hankali ba ita ka’dai ba ce.” Mami ta sakar masa dak’uwa ta ce “Ahmad ni kakar ka ce.” Murmushi ya yi yana sosa kai ya bar wajen. Nan kuwa Humaira ta tasa ni a gaba da tsokana sai da Mami ta tura ta wajen Umma tana furta tafi wajen Uwarki kafin ranki ya b’aci ba zaki wahalar min da y’a ba.” Humaira ta turo baki ta ce “Ni wai Mami me yasa kike min haka?” Mami harararta ta yi kawai. Yaya Faruk ne ya ce “AYSHA ina mijin naki Alhaji mai tumbin Naira?” Gaba d’aya suka saka dariya ni kaina dariyar nake. Na isa wajen Umma itama na rungumeta. Murmushi kawai ta yi tana furta “y’ar gidan Mami an dawo lafiya?” Humaira ta ce “Har na hango sanda kike wani irin huci idan kin ganni..”. Na kai mata duka da sauri ta isa wajen Mommyn Ustaz ta b’uya a bayan ta tana furta “Taimake ni Mamanmu.” Har muka isa gidana ina jikin Mami Ina sangartar da na da’de ban yi ta ba. Ita kuma sai ririta ni take yi. Tunda aka bu’de wawakeken gate d’in nake binsa da kallo. Wani irin gida ne mai kyawun gaske da ya sha farin paint da adon bak’in k’arafa da k’ofofi da winduna. Ba k’aramin tafiya da Imani na gidan ya yi ba. Shuke shuken da suke gidan sun matuk’ar sake k’awata gidan. Daga gefen wajen parking space muka yi parking. D’ayan gefen kuma wani k’ayataccen garden ne da ya yi kyau sosai. Hannuna cikin na Mami na muka shiga gidan da ban san yaushe Ustaz ya gina shi ba. Kyau da tsarin gidan kam ba’a magana. Kamar Ustaz ya san irin gidan da nake mafarkin Mijina ya mallaka kenan. Sai gashi Allah ma ji rok’on bawa ya cika min duka burina na duniya sai dai fatan dacewa da samun tagomashin Aljanna. A babban parlorn gidan aka baje ana ta zuzzuba abinci. K’amshin abincin ne ya ishe ni na mik’e da sauri na shige wani bedroom da yake can lungu. Mami ce ta biyo ni don dama Mommyn Ahmad da Ummanmu basu zo gidan ba. A toilet ta ganni ina ta kakarin amai tana shigowa Ustaz yana biyo bayanta. A tare suka dinga min sannu hakan ya bani dama na sake narke wa na kwanta a saman gadon ina mayar da numfashi. Mami ta kalli Ustaz ta ce “Kun je asibiti kuwa?” Ustaz ya d’aga mata kai hankalinsa duk a tashe. Mami ta jinjina kai tana furta “Sai a hankali shi ciki mai laulayi haka yake, Allah ya raba lafiya Amma dai AYSHA ki dinga daurewa. Jeka ka samo mata lemon tsami ta matsa a bakinta.” Da sauri Ustaz ya fita. Mami ta kama hannu tana min tausa a hankali. Wannan ne ya bani damar jefo mata tambayar da tun d’azu nake fargabar amsarta. “Mami kin koma gidan mu ne?” Ta girgiza kai fuskarta a d’aure ta ce “Ban koma ba, ba kuma zan koma ba, yanzu ma hutu na zo daga England.” Na turo bakina ido na suna cika da hawaye. Na janye jikina daga nata. mami ta bu’de baki tana kallona cike da mamaki ta ce “Au Har yau baki girma da shegiyar shagwab’ar taki ba?” Kuka na saka mata sosai bata rarrasheni ba kallo na kawai ta tsaya tana yi. Sai can ta ce “Da wannan sangartar AYSHA zaki haifi d’an da zaki masa tarbiyya?” Na turo bakina na ce “To ba na ce ki koma kin k’i ki koma ba?” Dariya ta tuntsire da ita kafin ta ce “MAFARKI DA BURIN AYSHA YA CIKA na koma gidan ku, me za ki ba ni?” Wani irin sufa na yi na shige jikinta Cikin matsananciyar murna na furta “Alhamdulilah! Mami na how comes Ban ji labari ba?” Ta gyara zamanta tana furta “Kawai dai na gaji da magiya da nacin Abbanki da Ummanki da Aiken da yake gidanmu, hakan yasa na hak’ura na koma. Bayan na tabbatar da nadamar Abban Ayshatu.” Murmushi na saki ina goge hawayena bayan na gama jin bayanin Mamin AYSHA na komawa gidansu AYSHA. Mami ta share min hawaye na, tana furta “Na sani AYSHA, na San duka zuri’ar gidan ku suna so na sai dai shai’dan da yaso ruguza dukkan farin cikin mu. Alhamdulillah a farko ya ci galaba akan wasu daga cikinmu sai dai ni tun a farkon da zuciyata ta yi zafi na zauna na yi tunanin ko nice a shoe d’in su irin zargin da zan yi kenan, sai na ji na samu nutsuwa, na kuma cire k’ullatar da na musu, na dinga addu’ar Allah ya bayyana gaskiya, Ya wanke ni da ni da ke daga zargin da ake mana. Alhamdulillah addu’a ta ta karb’u a lokacin da na yi tsammani.” Na ja ajiyar zuciya bayan jin jawabin Mami. Na rungumeta a jikina ina jin tausayin abubuwan da aka dinga mata a wancan lokacin duka a kan laifin da ba nata ba. Daidai lokacin Humaira ta shigo turus ta yi sai kuma ta juya tana dariyar da ta riga ta zame mata jiki. Mami ta k’walla mata kira, Amma ta k’i dawowa ta furta “Ba ruwana Mamin AYSHA, ba mai shiga tsakanin uwa da y’a a sha hirar yaushe gamo lafiya…” muka yi dariya ni da Mami muna furta “Humaira kenan!” Mami ta ce “Ai Ummanta ta riga ta sangarta ta. Wancan satin fa kwananta bakwai a gida wai tana gudun mijin sai da Muhammad ya mata jan ido ta tafi.” Na ce “Mami ai baki ga komai ba, sai loakcin da ta dawo a bayan Umma nanik’e da ita take barci.” Mami ta ce “Ikon Allah, kamar ke kenan, da fa ba kya iya barci sai a jiki na.” Na yi murmushi kawai ina furta “Na fi samun nutsuwa ne idan ina jikin ki Mami, sai na yi barci hankali kwance,da ba kya nan fa da k’yar na Saba.” Mami ta ce “Ai hakan yana saka shak’uwa da soyayya tsakanin iyaye, idan mace ta yi aure kuma sai ta koma bayan Mijinta. Hakan yana saka soyayya mai zafi a tare da su. Ta yarda ko fa’da suka yi ba zai yi tasiri ba zasu shirya don ba zasu iya kwanciya ba tare da juna ba, ki kula da wannan Ayshatu.” Na jinjina kai. Ina rufe fuskta a jikinta. Ta d’aga kai na tana furta “Ke tsaya wai ni kike jin kunya? To ki cireta don a wannan zamanin idan uwa bata koya wa y’arta zaman aure ba tsaf za’a gurb’ata mata tunaninta don haka kika ga tun da bana jin kunyar koya Miki komai. Kada ki manta ni na koya Miki saka Bra pad da sauransu. A gabanki nake saka turaruka duka lungu da sak’o na jiki na don ki gani ki koya ke ma. Don haka ki cire wata kunya a ranki na gaya Miki.” Sai dare suka shirya suka tafi. Duk sai na ji hankali na y’a tashi ganin za su tafin Har hawaye na yi. Ustaz ya ja hannuna duk sai na ga jikinsa a sanyaye shi ma. Sai da ya tabbbatar na ci abinci na sha magani sannan ya shiga wani bedroom na ga ya fito ya dawo ya zube a gaba na. Kansa ya saka a cinyata tsawon minti guda kafin ya d’ago. Idanunsa sun ka’da Sun yi jajur ya kama hannuna ya matse da k’arfin gaske murya na rawa ya ce “Zan tafi AYSHA!” Wani irin waro ido na yi zuciyata na bugu na ce “Zaka tafi ina?” Ya furta “Wajen Hameedah..”. Yana lumshe ido hankali na a tashe nake bin bakinsa da ya furta Hameedar da kallo. Zuciyata na ji tana wani matsanancin bugu don sai a lokacin na tuna ba ni ka’dai nake da shi ba. Cikin wata irin murya mai rauni na ce “Na shiga uku Ahmad wannan kuwa ba zai zama ajalina ba, wani abu nake ji a k’irji na….” Jikar Nashe★✍️ [10/16, 5:45 PM] Aunty Nazeefa 🥰: NA GA RAYUWA….LAST PAGE💃💃 ALHAMDULILLAH…… Godiya ta musamman ga Ahalin gida na Musamman Wanda suka yi patronising NA GA RAYUWA. Na gode k’warai Allah y’a yi muku sakamako da mafi alherin sakamako. Sai y’an comment section da basa gajiya da suburbu’da comments . AYSHA, MAMIN AYSHA DA USTAZUN AYSHA NA GODIYA. 🥰 NAZEEFAH SABO NASHE★✍️ 08033748387. Wani irin kuka na saki, ba na komai ba sai na zallar farin ciki da samuwar ciki a jikin Mami, abinda aka da’de ana nema. Na rungumeta sosai a jikina ina sakin kuka mai ha’de da murmushi… ina kallo Ustaz ya d’an saki murmushi ya fita waje. Umma ma cikin dariya ta ce “To meye na kukan? Madadin ki dinga furta Alhamdulillah? Ai godewa Ubangiji shine abinda ya kamata yanzu.” Ajiyar zuciya na saki na ce “Kukan farin ciki ne Umma, wallahi ban tab’a Jin irin farin cikin da nake ji yau ba.” Umma ta ce “Na sani Aysha, haka kowa ma yake wannan farin cikin, duka gidan nan murna muke da wannan lamari mai girman gaske, wa ya isa ya maka wannan banda buwayi gagara misali a sanda ka cire rai a lokacin kuma Allah ya kawo saboda ya nuna mana komai akwai lokacinsa, fatanmu Allah ya raba su lafiya.” Na ce “Ni fa da Umma na yanke shawarar da zarar na haihu zan dank’awa Mami abinda na Haifa wallahi. Ta raine shi kamar yarda ta raine ni.” Mami murmushi ta saki ta ce “Ai ko yanzu ma zan yi farin ciki Aysha idan kika ba ni na raini jika na na farko.” Na saki murmushi na ce “In sha Allah Mami. Sai su tashi just like twins shi da Uncle d’insa.” Haka muka zauna aka dinga hirar Mami cike da farin ciki muna shirya irin gagarumin taron sunan da za’a yi. Sai dare Ustaz yazo muka tafi gida ko a gidan ma na ishi Ustaz da zancen cikin Mami. Shi dai murmushi kawai yake. Bayan watanni shidda…….. Abubuwa da dama Sun faru Sun wuce. Wasu masu da’di wasu kuwa sai dai godiyar Allah. Sosai nake samun kulawa da tattali da soyayya wajen Ustaz da yake ji kamar ya mayar da ni ciki. Ko motsin kirki baya bari na na yi musamman girman cikin ya isa kwatance. Nauyinsa nake ji sosai, ya kumbura ni ya sauya min duk wata halitta da take jikina. Shirin tafiya yake mana zuwa Egypt don na haihu a can, tafiyar da yake shirya mana har da Mami na, da Mommynsa sai Khadija k’anwarsa da zata taya ni zama a can. Barcin la’asar sakaliya na ke sosai a parlor kan wata kujera mai taushin gaske. Na ji kamar ana ja min hanci hakan yasa na Ware ido na ina kallon Ustaz da yake tsaye sai murmushi yake min fuskarsa cike da walwala. Ya mik’a min hannu. “Taso y’ar beauty…” dariyar da yake ne yasa na san tsokanar da y’a Saba min zai min, hakan yasa na turo bakina. Tunda cikina ya tsufa yake tsokanata da sunan Beauty. Zama ya yi yana rab’ani da jikinsa ya furta “Sowie dear, albishir fa nazo Miki da shi k’in saka zan manta.” Da sauri na kalleshi na ce “Albishri d’in me?” Ya ce “Ke dai albishirinki…” na ce “Goro.” Bakinsa ya nuna min yana murmushi hakan yasa na manna bakina da nasa don na San abinda yake nufi. Kyakykyawar kiss na bashi. Ya lumshe ido yana murmushi ya sake ja min hancina da ya tashi sosai ya furta “Aysha cikin nan ya maki kyau, ji fa hancinki da bakinki yarda suka sake doubling size d’in su.” Pillow na d’auka na wurga masa ina turo baki na ce “Ustazu bana so!” Murmushi ya saki yana furta “Ayshatu, ina so. Ba kya son na gaya Miki albishir ‘din?” Na turo bakina ido na ya yi raurau don gani nake kamar da gaske Ustazun muni na yake gani. “MAMIN AYSHA.. ta haifi twins Girls….” Wani irin waro ido na yi kafin na ce “Are serious Ustaz?” Ya d’aga min Kai yana murmushi ban San sanda na isa na rungume shi ta baya ba ina furta “Ka zo min da kyakykyawan albishir I love you dear…” Shukaran lillah.. ya furta a hankali yana pecking goshi na. Da Kansa ya zira min Hijab muka fita don zuwa wajen Mami na da nake jin kamar na yi tsuntsuwa na je wajenta. Da hawaye na na shiga gidanmu ina tunanin Ashe za mu ga wannan rana? Ashe Mami za ta daina amsa sunan Juya a wajen dangin Miji? Tabbas bayan wuya sai da’di. A zaune na samu Mamina na isa wajen na zauna a gefenta cikin murmushi na furta “Alhamdulillah Sannu Mami.” Ta Shafa min Kai na ta ce sannu Ayshatu… Allah ya rabaku lafiya Allah yasa kada ki sha wuyar da na sha.” Ameen na furta jiki na a sanyaye kafin na Kai hannu na d’auko babies d’in masu tsananin kyau kamar ni ina jaririya Sun sha fararen kaya masu kyau gaske. Da sauri na kalli hoto na da yake gefen gadon Mami hotona ne ina jaririya na ce “Wallahi Babie d’in nan da ni suke kama.” Abba d a yake tsaye ya saki murumushi ya ce “Ba sai kin rantse ba Aysha, ai tun d’azu Nima na fa’da kama suke da ku sosai.” Na rungume su a jikina da k’yar Abba ya ce na bada su a kaiwa Ustaz. Kafin ka ce meye wannan gidan mu y’a cika dank’am da mutane. Y’ay’a da surikai da jikokinsu haka aka cika gidan taf ana taya Mami murna, tabbas haihuwa rahma ce kuma ina tausayawa Wanda bai yi ta ba, sai dai kuma akwai ladansa mai girma a wajen Ubangiji ba mamaki y’a zama sanadiyyar shigarsa Aljanna. Sanda Ustaz yazo don mu tafi dagawa na yi anan zan kwana. Abba ne ya ce tilas sai na fita na bi Mijina kwanan me kuma zan yi? Haka na tafi duka raina a b’ace. A mota Ustaz yake sanar da ni Visar mu ta fito. Na jefe shi da hararar wasa na ce “Kai ma ka San ko birnin lantsandan ne ba zani ba, har sai an yi suna.” Ustaz ya ce “Kada mu yi haka da ke K’alb, tunda dai t haihu lafiya ai shikkenan.” Na turo baki na ce “Kada ma ka fara, Am serious I won’t go anywhere…” shiru ya yi na lura ransa ne ya b’aci shi yasa bai sake min magana ba, ni kuwa ba zan sauka daga kan nawa ra’ayi nn ba. Haka muka kwanta yana Jin haushina dai dai bai fasa yi min duk abinda yake min ba. Ya bani abinci da drugs d’ina ya ha’da min ruwan wanka. Tsakar dare….. Cikin hukunci Ubangiji na ji baya na ya yi wata irin amsawa. Ba shiri na mik’e jin Mara ta ta amsa itama. Ban san sanda na d’aka wa Ustaz duka ba a gigice ina furta “Ka tashi mutuwata ta zo Ustaz, wayyo ka yafe min.” A Gigicen shima ya tashi. Yana kunna side lamp ya ce “Lafiya me ya faru?” Azabar ciwon da na sake ji ne yasa na damk’i hannunsa da k’arfi ina salati na ce “Mu tafi Asibiti Ustaz mutuwa zan yi..” da azama y’a zura min Hijab ya kinkime ni zuwa cikin mota don bana jin zan iya tafiyar ma. Ciwo kam na sha shi kafin mu isa asibiti, sai dai cikin k’udirar Ubangiji muna isa asibitin na haihu yaro namiji kyakykyawa jajir da shi kamar d’an larabawa. Farin ciki ne ya ratsa ni sanda na bu’de idona a kan fuskar yaron mai kama da Babansa kwabo da kwabo. Na furta “Alhamdulillah” cikin muryar da ta riga ta galabaita. Ahmad ne ya fara shigowa cikin d’akin. Idanunsa a kaina ba ya ta Babyn da ake mik’a masa cewa kawai yake “K’alb, hope dai k’alau kike?” Na gya’da masa kai ina murmushi sai da ya saka hannu ya kwantar min da gashin kaina da ya yi Buzu Buzu sannan ya amshi jaririn da likitan take mik’a masa. Manna shi ya yi a k’irjinsa yana sakin ajiyar zuciya kafin na ga ya manna masa sumba a lab’b’an sa a hankali ya furta “What a wonderful gift! Alhamdulilah ya rabb…” ya lumshe idonsa sai ga hawaye suna zubo masa. Na saki murmushi nima ina jin k’wallar na son zubo min. Ya bu’de idonsa yana sakin murmushi ya furta “Kyauta mafi girma, daga halittar da nafi so fiye da kaina a duniya….” Sai da aka gama shirya mu sannan Ustaz ya dinga gayawa Mutane na haihu. Na San kowa sai ya yi mamaki don na rage edd na da kusan sati uku. Kafin me, tuni asibitin ya cika da mutane, sam ba su wani duba tsakiyar dare ba ne. Yayyena duka sun zo haka Humaira Umma da Mami na, da ba yadda ba’a yi ta zauna ba Amma sai da ta zo. Humair sai ta tambayata take wai haihuwar da wahala? Murmushi na saki ina kallon turtsetsen cikinta na saki dariya na ce “Wallahi ki shirya ma, don ba na jin a duniya akwai ciwon da ya kai na haihuwar azaba..•” Humaira ta waro ido… Asubar fari aka sallame ni. Mami kuwa tana gefena bata la’akari da sabon jegonta sai kulawa take ba ni. Da nuna tausayawa. Sanda muka isa gida na Hajiyan Potiskum ce ta tilastawa Mami sai da ta tafi gida fa’di take “Tafi maza y’ar albarka ke ma ai d’anyen jego ne kike haihuwa kwana guda, sai sanyi ya kama yaran.” Haka Mami ta hak’ura ta tafi ba don ta so ba har a ranta. Haka aka cigaba da kulawa da ni. Gefe guda kuma ana ta shirin ha’da suna na da na Mami inda za’a yi shi a wani Babban wajen biki. Ranar suna da safe Ahmad ya sanar da sunan yaro Sulaiman sai muke ce masa AKBAR. An tari sosai a shagalin sunan. Inda twins d’in Mami suka ci suna NILFA DA NAUFA. Abba na bai ji kunya ba sunan Matansa Mami na da Umma na ya mayar. An sha suna an gaji jikina ya yi Lakwas. Hakan yasa muka yi wanka kawai muka kwanta. Cikin daren na ji Ustaz a jikina da sauri na bu’de ido ina kallonsa ina nuna masa Hajiyar potiskum da take zube a k’asa tana barci. Ya saki ajiyar zuciya ya ce “To tashi mu je, wata mahimmiyar magana za mu yi.” Ban yi musu ba na mik’e don ban hango wasa a idonsa ba. Ina shiga d’akin na gan shi yana parate a tsakar d’akin fuskarsa a ha’de sosai hakan da ya razana min zuciya. Na dinga kallonsa hankalina a tashe. Idonsa a kai na ya mik’o min wata farar enveloped na kalleshi na kalli takardar zuciyata na wani irin bugu. “Karb’i mana…” na ji ya furta muryarsa a sama. Hannuna na rawa na amshi takardar na bu’de ina addu’a ido na a runtse kafin na Ware ido akan takardar. Abinda na gani ne yasa Ban san sanda na daka tsalle na rungume shi ba takardun wata babbar plaza ce da yake ginawa shine ya mallaka min. Kiss na masa sosai kafin na ce “Na gode Jannaty, ka yi min komai…” muryarsa na rawa ya rungumeni yana furta “Ni ne da godiya K’alb, kin shayar da ni duk wani abu da nake so a rayuwar nan kin bani farin cikin da Ban tab’a zaton akwai shi ba. Ke mace ta gari ce Mumina mai halin k’warai duk Wanda Allah ya bashi mata irinki a duniya to fa ba shi da wani sauran buri a duniya sai dai ya yi fatan dacewa da lahira… Allah ya yi Miki albarka K’alb…..” Ya fa’da yana manna min kyakykyawar sumbata a bakina. A hankali ya janye daga jikina yana furta “Madalla da Mace ta gari, Alhamdulillah.” Nima na ce “Madalla da Miji na gari Alhamdulillah!” A tare wasu hawaye suka zubo mana. Tabbas rayuwar mu ta yi kyau Allah yasa mu dace. Jikar Nashe ma anan take cewa Alhamdulilah sai mun ha’du a sabon littafina HADARIN GABAS…. Ga wanda yanzu suka fara bin littafina akwai wasu a k’asa. Masu tambaya… Takaicin Uba….. labarin yarinyar da ta rasa dukkan farin cikin ta sanadiyyar mahaifinta. Ayra Gaya an sha gumurzu kafin ta amince ba duka maza ba ne suke amsa sunan Butulu…. Tabbas mijinta ya sha fama kafin ta amince ta amshe shi a matsayin miji saboda tsanar da ta yiwa Ubanta. Idan baki karanta ba 1k ne Amma ina promo zan ba ki shi akan 500 kacal. Ya Abin Yake? Labarin yarinyar da Uwar ta ta tsaneta sanadiyyar wani b’oyayyen sirri da ita ka’dai ta sani sai Hammad da ya zamo d’a ga Mijinta ashe akwai k’ura a lokacin da Hammad ya bayyana kansa a matsayin Mijin Hamda da suke Uba d’aya. Anan allura ta tono galma… Me Zan Yi da ita? Littafin da ya kara’de duniyar rubutu. Gaskiyar Lamari… K’udirar Allah…. Mhmmn wata miyar sai a mak’ota. D’AND’ANO DAGA KUDIRAR ALLAH. LITTAFIN NAZEEFAH SABO NASHE. PAID BOOK IDAN KIN SHIRYA SIYA TURA KUDIN KAI TSAYE A ACCOUNT NUMBERR NAN. 2118666253 UBA KI TURA SHAIDAR BIYA TA 08033748387. Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban tab’a kusantar wata mace ba?” Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta “Tabbas Jaheed jininka don gwajin k’wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun tabbatar da Hakan koda Ba’a yi gwajin ba.” Shiru na tsawon lokaci d’akin ya d’auka kowa da irin tunanin da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da k’wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai tab’a rik’ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d’ansa ne ta yaya ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai tab’a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD’i. Mahaifiyar Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi. Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K’UDIRAR ALLAH…. Ya zama complete biya 1k kacal don ki karanta. SARAUTA TA DANNO. SHAHARARRIYA MARUBUCIYA NIMCYLUV ZATA ZO MUKU DA SABON LITTAFINTA MUTALLAB 1.10.2024. SAURA KWANA BIYU💃🏿 HANZARTA SHIGA GROUP DON KARANTA LITTAFIN DA BA NA BIYUNSA A WANNAN SHEKARAR…. Domin a fara tafiyar littafin *💋MUTALLAB💋* da kai join our Conversation group. Musamman iyaye mata wanda yaransu ke age ɗin Adolescence https://chat.whatsapp.com/GjfdfXJ0Pg0HGgCT0UkCt5 Na yi gaba sai kun zo 💃🏿💃🏿