[12/16, 8:19 PM] Hassan: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* Page 1 ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU AYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ _karamacinki da alkharinki tattare da mutuncinki gareni, ba zai misaltu ba, aunty ummi nah , ina sonki irin soyayyar da 'yan'uwantaka kad'ai ke haifar da hakan , ina rokon Allah ya barmu taren tare har karshen rayuwarmu, Allah ya k'ara damkon kauna da zumunci atsakaninmu, love you so much my special aunty ,kaf media babu aunty tamkar ki ,shi yasa zan sadaukar da gabadaya novel dina gareki domin kin cancaci fiyye da hk a zuciyar bagudo_ alhamdullahi am back again. warning!!! for the first time !!!! i will like to say," don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people ,if you read it is for your own risk ..... WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim ....Ayshatul muwaddat kwance take akan lafiyayyen gadonta kiran italy, amman ba bacci take yi ba, kurun dai ta kwanta ne tana tunanin Muhammad auwal ne bisa tsarin zuciyarta. cigaba tayi da tunane tunanen zucin data Saba, Wanda ya rigada ya zame mata jikinta ,a duk sanda ta ke'be kanta to fa Bata da wani aiki sai na tunaninsa, yayinda zuciyarta zata yita kissama mata yadda sufofinsa jikinsa suke had'e da yanayin tsarin rayuwarsa ,komai nashi Yana matukar burgeta most especial sautin muryarsa Mai shiga jiki da tsayawa arai ,da tsarin halittarsa , naunayen ajiyar zuciya ta sauke da karfin gaske had'i da lalibo wayarta dake ajiye a saman bedside tashiga neman layinsa . Kira daya biyu ya d'auka cikin sanyayyiyar muryarsa "hello Aysha nah .. .... Tana jin sautin sanyayyiyar muryarsa mai shiga jiki ta lumshe idanunta, tana fesar da numfashi saboda wani Abu da taji ya tsarga mata tun daga cikin kwakwaluwar kanta har zuwa kasanta ya dinga yawo a koina a sansar jikinta. Shiru sukayi gabadaya batare da kowanensu yayi yunkurin furta wani Abu ga d'an'uwansa ba ,illa numfashi da ajiyar zuciyar da suka dinga saukewa a tare Yana ratsa kowani Shashi na gangar jikinsu . Jin tayi shiru taki magana yasa yayi karfin halin fixgo magana yace "Aysha nah kin kirani sannan Kuma kin yi shiru , gashi zuciyata na sanar min da cewar akwai abinda bakinki yake son fad'i shiyasa Kika kirani ,me ke damunki ?"ki sanar min da damuwarki kinji .... Tayi shiru tsabar miskilanci dake cinta ,duk da dai maganar take son yi Amman harshenta yaki sarrafuwa Gurin lankwasa shi ,har sai daya sake yin magana "ki sanar min da damuwarki Aysha nah , domin sanin haka shi zai sa na samu natsuwar zuciya, akasin haka Kuma kin san tashi hankali ne gareni , Dan haka kiyi hakuri ki sanar min kinji ta hannun damana. Jin yadda ya wani marairaice mata yasa ta bud'e bakinta da kyar tace "babu komai fa kawai dai na Kira ne mu gaisa " kinyi kewata ko ? "kewarka Kamar ya kenan ? "Kamar dai yadda Kika Saba ya bata amsa yana buso mata numfashinsa "ta numfasa kana tace "a'a ni ban yi wani kewarka ba . Yayi laulausar murmushinsa dake k'arawa halitar fuskarsa kyau yace "ban yarda ba akwai dai abinda zuciyarki take 'boyewa . tayi shiru taki yin magana, ya lumshe tsumammun idanunsa yana tunaninta ,ya santa yasan halinta ba tun yau ba, saboda kusanci dake tsakaninsu, iya shakuwa sun shaku daita fiyye da tunanin Mai karatu ,Amman duk da wannan shakuwar tasu, hakan ba yasa ta sake dashi a waya, har gara ma idan suna chatting ne ta kan saki jikinta dashi sosai tayita Masa Hira , wani lokacin har mamakin hakan yake, bud'e idanunsa yayi ahankali ya cigaba da magana na tsawon second biyu sannan yace "tunda kin yi magana mu had'u a what's app ....ya katse kiran . batare da 'bata lokaci ba,kai tsaye ta kunna datanta sannan ta shiga contact dinsa inda cikin sanyayiyar muryarta tasoma masa voice ... "auwal kanina ya kake? "ya karatu hope komai na tafiya daidai ? ba kamar yadda ni na tsinci kaina ba, gabad'aya bana jin dadin rayuwata saboda rashinka kusa dani, ta tura masa sakon ta koma ta jingina da abun gadon tana Mai runtse idanunwata kad'an, zuciyarta na wani irin harbawa da sauri sauri . can kmr minti biyu sai ga sakonshi yashigo ,da sauri ta zabura ta gyara zuwa kwanciya, sannan ta kunna vioce din daya turo mata , tare da manne earpiece a kunneta saboda tsaro ,ahankali ta soma sauraron sakon daya turo mata. jin zazzakar muryarsa yasa take ta sake shiga cikin wani yanayi na daban . "Muwaddat kenan daman nasan akwai abinda ke cin ranki ,nima wallahi bakiji yadda nake jin kaina adalilin nisan danayi dake ba, ji nake tmkr bani tare da wani kuzari a bangaren rayuwata , dan Allah ki fad'a min yadda kike ji akaina ina son sani ..? tayi shiru taki cewa komai illa zuciyarta da gangar jikinta da suka sake shiga cikin shaukinsa ..... "kinyi shiru hope kina cikin koshin lfy dan banason jin yanayinki irin haka plz talk to me my muwaddat? amadadin tayi masa voice kmr yadda suka saba sai tayi masa typing "uhmmmmm, share kawai kanina nagode sosai da kulawarka sannan babu abinda ke damuna .. .. "nidai a'a ban yarda ba , sai kin fad'a min ko nayi miki kuka ya turo mata sako tare da alamar yar bbyn nan mai zanen kuka.. 😭😭 hotonsa dake kan dp dinsa tabi da wani irin shu'umin kallon sha'awa ,a sukwane ta tsurawa k'aramin bakinsa ido, tana kallo tmkr ta kai bakinta ta tsotsa haka ta dinga ji, ta d'auki tsawon minti goma kafin daga bisani tayi zooming din hoton ta tsurawa hoton kyawawan idanunta tsawon minti biyar tana kallonsa sannan ta koma contact dinsa "me yasa baka son kallon camera a duk sanda xaka yi hoto? "saboda tsoro ne kawai ,kana yayi murmushi kmr yana gabanta "kina son na kalli camera saboda ki kalli k'aramin bakina ko? ta tura masa alamar gwalo ganin har ya harbo jirginta ."muwaddat ya kira sunanta muryasa cike da matsanancin shaukinta da rauni mai raunata zuciyar duk Wanda ya saurara , "na'am M.A" dan Allah alfama nake nema agurinki " "na me kenan M.A ..? sai daya kashe muryarsa sosai sannan can kasa kasa yace "akwai wani project dana keyi anan London Wanda yake bukatar taimakonki , shi wannan project din Yana bukatar siffar jikin matashiyar mace, to gabadaya narasa yadda zanyi da rayuwayata, saboda ban San inda zan samo macen da zata yi min wannan taimakon ba . Cikin zakuwa tasoma rubutu" menene shi M.A ? "Idan na fad'a Miki Zaki min shi, bazaki zuba min kasa a ido ba ? "Ka fad'a min kawai ni Kuma nayi alkawarin matukar ina dashi zan baka shi "I you sure mu muwaddat zakiyi ? "zanyi mana , karka ji komai kai dai fad'a min abun? sannan me yasa ma kake dauting Akan bazan yi ba ? "M.A kafi karfin komai agurina ,babu abinda bazan iya maka ba ,bare wannan daya SHAFI bangaren karatunka ka fa'da min kawai ." Yana gama karanta sakonta take jikinsa yasoma sanyi yana macewa ahankali tun bai kai ga furta mata ba, yayinda gabadaya ilahirin tsigar jikinsa suka Mike tsaye , ahankali ya soma typing "nonuwanki kawai nake son na kalla ahalin yanzu, plz karkice min a'a kinji muwaddat " ya tura mata ,Yana tura mata ya goge ya sake rubutawa ya goge yayi haka yafi sau biyar, sannan daga karshe yayi kundin Bala ya tura mata ya koma ya jingina bayansa da pillow Yana jiran amsarta .. .. Lokacin da sakon yashigo ta tsurawa kalmar nonuwanki kawai nake son na kalla a halin yanzu shanyayyun idanunta tana kallo tana maimata karantawa ,ta karanta sakon yafi sau goma ,Kamar wani karatu ,kafin kace me tuni kalmar tasamu kyawawan mazauni acikin kwalkwaluwarta ,gabadaya tarasa yadda zata yi gashi ta rigada tayi Masa alkawari bugu da k'ari abun ya shafi bangaren karatunsa bazata so yasamu matsala ba . "sha kuruminka d'an kanina ta fad'i hkn tana mai zaro nonuwata duka daga cikin doguwar rigar dake sanye ajikinta. duka tantsatantsar nonuwanta suka bayyana sai sheki suke da daukar ido , ta d'aukesu ta tura masa cikin second biyu sakon vioce dinsa yashigo . wani irin ihu ya saki "ayshatul muwaddat na rantse da Allah ga nono ,wayyo Allah nah, wallahi kmr nasa bakina akansu na tsotsa, ga nipples din nan ya Mike tsaye , amman dai kina cikin tsananin sha'awata ne ko? "wayyo Allah muwaddat dina wallahi irin nonon Nan nake nema a tsaye ,cak tamkar an dasa shi ,dan allah ki barni na sha nonon nan ,randa na dawo, karki hanani sha kibarni naji tumin jikinki ko bazaki Bari naji dumin gidan dadinki ba, amman dai kibari naji dumin jikinki, ki barni nayi duk yadda zanyi dake dan Allah , idan na samu nono nan, na dinga tsotsa sai kin sha mamaki nah" "dan Allah kiyi min alkawarinsu duk randa na dawo, ki barni naji d'umin jikinki ' Nayi missing din d'umin jikinki .. "typing tasoma yi Masa "wallahi bana tare da wata sha'awa komai ni dai haka kan nipples dina suke, ai ko ma ba zaka gansu a zahirance ba, balle ka tsotsa ,yanxu na tura maka ne kawai saboda project Dinka if not I will . ya narkar da fuskarsa kamar zaiyi kuka Dan Sam bai ji dadin maganarta ba, sannan muryarsa a kasalance ya rubuta "Muwaddat wallahi gabadaya nonon nan ya tayar min da hankali ,yanzu ya zanyi na samesu azahirance ahalin yanzu? Tace "babu yadda za'ayi ka samesu sai dai kayi aure, idan kaci sa'a matar da ka aura na da irinsa fine ,idan kuma Bata dashi sai ka d'auki hakuri ka rungumi sorry... sauke naunauyen ajiyar zuciya yayi da karfi Yana cinza lip's dinsa, sannan yace "muwaddat baki da tausayi wallahi, idan ki kace ba zaki bani nonon nan na sha ba akwai matsala, kai dole ma, na sha wlh ko bakya so sai na sha, sai dai idan bamu had'u ba .... k'arar da k'aramar wayarta ta d'auka ne yasa tayi saurin tura masa sakon ina zuwa, sannan ta mirgina ta d'an mika hannunta ta d'auki wayarta , babanta ne yake son ganinta sai alokacin ta tuna bataje ba ,gashi Kuma tunda garin Allah ya waye ba taje ta gaida baban nata ba ,ta mike da sauri ta nufi matattakalar bene da zai sadata da falon babanta . matashiyar yarinya ce muwaddat son kowa kin Wanda ya rasa , kyakkyawa ce ajin farko wanda za'a iya sakata a cikin sahun farko na jerin kyawawa Matan duniya , duk da ba fara bace sol , amman muna iya kiranta da wankan tarwad'a, chocolate colour bambamcinta da farar mace kad'an ne ,doguwa ce mara kiba, ba kuma siririya ce ainun ba, tana da murjajjen jiki irin na ya'yan hutu kalar fatarta lu'kwi luk'wi masu zuba sheki, dara daran idanunwanta da dogon hancinta sun taimaka wajen fito da kyan fuskarta, tana da d'an k'aramin zagayayyen baki mai kyan fasali, kmr irin na Muhammad auwal ,game da fararen hakora kuwa ba'a magana ,kallo daya zaka yiwa muwaddat ka fahimci gata ya wadata tattare da shagwaba ajikinta , duk da fuskarta batayi Kama da shagwababbiya ba, Amman in kaga yadda take sakewa tana zuba shagwaba a gaban iyayenta sai kayi mamaki .... Yadda fasali da kyawun surarta take haka Muhammad Auwal yake kusan komai nasu iri daya bambancinta dashi ,shi fari ne sol ita kuma chocolate colour.. Mmn sudais [12/19, 11:01 PM] +234 806 956 2358: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU AYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ ~BEST AUNTY FOREVER AND EVER~ alhamdullahi am back again. warning!!! for the first time !!!! i will like to say," don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people, if you read it ,is for your own risk. WATTPAD @HAUESH BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM page 2 ..tana hawa benen mahaifinta, ta d'an zuge kofar glass din parlour'n tashiga bakinta d'auke da sallama, sai alokacin gaanta ya fad'i sakamakon tunawa datayi da kanta babu d'ankwali ,daga ita sai wata hadaddiyar doguwar rigar, yar saudiyya wacce ta sha stone work ,amman kanta babu komai ,hakan ne yasa dogon gashinta data had'a ta tufke da ribbon suka bayyana . har ta shiga parlour'n tana fargaban fad'an da dad dinta zai yi mata idan yaga kanta babu dankwali, jikinta a sanyaye ta k'arasa gaban dad ta d'an durkusa ta gayar dashi kana tace" dady gani . alhaji muhamud mai agogo ne zaune cikin tangameman parlour'n shakatawarsa, wani d'an k'aramin table ne agabansa, cike da kayayyakin motsa baki iri iri.. alhaji Muhamud ya d'an d'ago ya dubi yarsa muwaddat cike da fara'a da sakin fuska, sannan yace "muwaddat me kike yi acikin gidan nan tun safe baki lekoni ba . tsadadden murmushinta tayi sannan tace dady babu abinda nake kawai a kwance nake, ina d'an hutawa, jira nake sai ka sauko sai na gaisheka. " ok babu damuwa ince duk kanen naki sun tafi makaranta ne? "eh sun tafi har ma direba ya dawo "to mai maman taku takeyi da bata zo ta kwashe wad'an kayan abinci ba? "dady wanka tashiga, amman nasan zuwa yanzu ta fito" yace" yanzu hk baki ci abinci ba ,kika je kika kwanta ,maza ga abinci nan ki zauna kici "dady bana jin yunwa ,ni bama yanzu zanci abinci ba . "anya muwaddat kina kyautawa rayuwarki tunda kika xo gidan nan kullun sai ayi miki fad'a akan cin abinci amman bakya ji, wai ke yar gayu ko ? tayi murmushi kawai, shi kuma yaciga da mgn "ina kika ta'ba ganin ana gayu ciki babu komai. ta sake yin murmushi sannan ta mika hannunta ta d'auki apple guda d'aya ta kai bakinta ta gutsura tana niyyar tashi yace "ba tafiya zakiyi ba, ki zauna ina son muyi magana dake" ta mike cikin natsuwa ta koma kan d'aya daga cikin kujerun na alfarma dake zagaye da parloun ta zauna tana jiran abinda zai gaya mata. ya dubeta kana yace "muwaddat me yasa baki son d'aura d'ankwali? " wato kin fi son kullun sai na miki fad'a akanshi ko? "tace dady kayi hakuri wallahi mantawa nayi kuma kaina tsantsi garesa idan na d'aura d'ankwali baya zama sai yayita zamewa yace "zaki san gashinki mai tsantsi ne duk ranar dana saka aka aske miki kan na gata gayu.. muwaddat ta d'an langwa'be kai a kujerar tana dry yake, tasan fad'a kawai yake bazai iya aikata hakan ba.. "au gani kike da wasa nake yi, shi yasa har kike dry ko? cikin shagwaba tace "to dady to ita umminah tana ina da har zata bari a aske min gashi? "ai tunda bakijin magana daga ke har ummin taki na daina saurara muku tunda bata iya kwa'barki komai kike so sai ta biye miki, nan gaba in kuka yi wasa agaban ummin taki zan sa bulala in zaneki in ga yadda zatayi "a'a d'an Allah dady kayi hakuri na tuba bazan sake ba , in dai kan d'ankwali ne daga yau zan dinga d'aurawa " sukayi 'yar dariya gabad'aya sannan yace "wai kuwa kinsan ma abinda nake shirin yi miki magana akai ? ta girgiza masa kai "bansani ba daddy "yace to karatu nake son na samar miki a jamiar United Kingdom ... muwaddat tayi saurin dafe daidai saitin zuciyarta dataji yayi wani irin mahaukacin bugu da karfin gaske, saboda tsanar karatun da tayi ,a tsarinta sam tafi bukatar yin aure akan wani karatu, ta girma da muradin son yi aure da wuri saboda yanayin halittarta ,sai dai tsawon lokacin nan bata samu wanda yadace daita ba kmr kaninta auwal wanda take ganin da wuya ta mallakesa arayuwarta, tunda ta kammala karatunta na diploma ,ta cire rai da wani karatu, nest budget dinta shine aure,ita aure take so ba karatu ba. sai dai ahankali zantuttuka mahaifinta ke shiga cikin kunneta kafin daga baya tace "wani irin karatu kuma dady ? "nifa banida muradin tsanata karatu mai zurfi" "kin ci gidanku dole kiyi karatu mai zurfi domin shine burin mu iyayenki, na asali da iyayen goyonki ,guda nawa kike yanzu da zakice baki da muradin karatu idan bakiyi karatu a halin yanzu ba uwar me zakiyi? aranta tace "aure mana daddy ...... " yanzu ne daidai ki natsu ki tsaya kiyi karatu amatsayinki na yarinya yar shekara ashirin da haihuwa "daddy ni dai banason karatun nan yanxu kabarni kawai iya dilomar ma dana ta isheni .. " "haba muwaddat ni fa nafi son kiyi karatu mai zurfi Allah yasani, "to da kika nace baki son karatu,aure kike so ko me ? muwaddat ta d'an noke kai ala'mun jin kunyar mgnrsa tana dry "kinga nifa Allah yayoni da mugun son karatun boko bansani ba kodan nasan dadin karatun ne? "ki taimaki rayuwata dataki ki cigaba da karatu, kafin muwaddat tace wani abu hjy hajara tashigo parlour'n wanda tun kafin ta k'arasa shigowa parlour'n take jin yadda alhj yake jaddawa muwaddat zance karatu mai zurfi yake son tayi. da sallama tashigo parlour'n tana "cewa ka rabu da wannan yarinya mara wayo kawai ,in da kai ya waye da karatu nan ,shine ita take cewa bazatayi ba, tasamu guri ta zauna tunda bataso "idan bakiyi karatu ba uwar mezakiyi uhmmmmm? "ki duba kiga yadda mata suka samu cigaba a dalilin karatu mai zurfi, ita kanta ummin taki tafison kiyi karatu mai zurfi kafin aure,amman shine dan iya shege kike cewa baki son karatu? "baki son karatu sai me? muwaddat tayi shiru tana jin kmr fito ta sanarwa da iyayenta burin zuciyarta, amman kunya tattare da fargaba ya hanata "ki dai gaya mata gsky karatu na da mutukar mahimmanci agurinta bari ummintata takaraso muji mai zatace, alhj muhamud na gama fad'ar hk ya mike tsaye ya sa kai ya fice yana takaicin rashin son karatun da muwaddat take yi... a harabar gidan yaci karo da motar dataje d'auko kanwarta da suke ciki daya, direban gidan na k'ok'arin daidaita tsayuwar motar yana ganinta ya fad'ad'a faraarsa sannan yaja ya tsaya yana jiran fitowarta, hjy mukarama ta fito a natse tana sanye cikin shiga ta alfarma doguwar riga ce har kasa sanye ajikinta da madaidaicin hijab, amman kallo daya zaka mata kasan cewar akwai gidan rana da tsantsar gogewa irinta 'yan boko atattare daita. ta k'araso ahankali inda d'an'uwanta yaja ya tsaya yana jiran k'arasowarta "kar dai fita zakayi Yaya ? "eh fita zan yi wai kafin ki karaso,dama wacan 'yar taki ta nemi 'bata min lokaci da tuni na bar gidan " "me kuma baby muwaddat tayi ? "da ita kullun bata wuce laifi agurinku shiyasa sam bata son zuwanta garin nan amman nake matsa mata " "ai duk ke kike d'aure mata gindi amman nasan yanxu idan kika ji abinda tayi sai ranki yafi namu 'baci yadda nasan kike da kulafucin son tayi karatu.. "au akan karatu ne? "akan shine mana wai yanxu nake mata maganar sai cewa tayi ita bata da muradin cigaba da karatu" hajiya mukarama tayi murmushi tace "manta da wannn shirmen nata karatu d'an ada tayi sa, dan ma inaji tsoron gur'bacewar da rayuwa tayi yanxu ,ai da tare aka had'asu da bunayya " "nima abinda naso kenan amman naga kamar ita bada raayin ma yin karatu, ni dai zan fita idan kin shiga kinsan yadda zakiyi daita " "ai tafiya ma zamuyi zaman shirun ya isheni ni kad'ai a gidan daman itace abokiyar hirar tawa sukayi sallama yayi hanyar waje ita kuma ta k'arasa cikin gidan ********* alhaji mahamud shine asalin mahaifin muwaddat, sai dai ba a hannunsa ta taso ba, ta girma ne a hannun k'anwanrsa da suke uwa daya uba daya , wato hjy mukarama da mijinta alhj ishaq , hjy mukarama da mijinta suna mugun son muwaddat ,babu irin kulawar da gatan da basu nuna mata ba , ko d'an cikinsu albarka . su biyu kawai iyayensu suka haifa suka mutu suka bari a duniya, mahaifinsu tun mukarama na k'arama ya rasu ,suka cigaba da rayuwarsu da mahaifiyarsu, sun sha gwagwamaryar rayuwa kafin daga baya mahamud ya isa munzali mutun, d'an ma mahaifiyarsu jaruma mace ce ,ta iya sana'oi iri iri ,da hk ta raini ya'yanta , sai dai shi mahammud bai samu damar karatun boko mai zurfi ba asanadin matsananciyar rayuwar da suka riski kansu a wancan lokaci ,iyakarsa secondary school kawai ya tsaya wanda yayi a karamar hukumar koko , domin alokacin primary school kad'ai ce a kauyen nasu babu secondary, sai dai akai mutun wani gari, sai dai hkn bai hanashi jajircewa na ganin kanwarsa tasamu karatun ta kowani bangare ba. bayan mahammud ya gama makarantar gaba da primary, ahankali ahankali yake sanarsa ta kwadago ta hanyar kasuwanci,da farko dai gyaran agogo yake har Allah yasanya masa albarka ya bunkasa arzikinsa ya zamo wani abu .. adalilin wannan sana'ar tasa yasa yayi suna ciki da wajen kauyen har ake kiransa da muhamud mai gyaran agogo, wanda duk inda zaka shiga a fad'in kauyen nemansa, matukar baka sanya lakaninsa ba ,sai dai ka gama karad'e kauyen babu mai ce maka yasanshi. bayan wani lokaci sai mahaifiyarsu ta kamu da ciwo ajali ta sha jinya sosai ,suka rasa yadda zasuyi, gashi ciki da wajen kauyensu babu asibiti sai anjen wani gari mai kuruna dake makwabta taka da kauyensu ,idan akace za'a kai mutun asibin ma zai iya yiwuwa ya rayu domin kafin akarasa mararrabar garin mutun zai iya mutuwa , nawa nawa akayi akan idanunsu suka gani ,dan haka addua suke kullun Allah ya kawo musu d'auki daga gwanati mai ci alokacin data tallafi rayukansu ta gina musu asibiti da makarantar gaba da primary . tunda mahaifiyarsu ta fara ciwon take barwa d'anta wasiyya a kullun bakinta baya shiru da mgnr diyarta mukarama ta kance "mahamud ko na mutu dan Allah ka kular min da 'yar'uwarka kaga bata da kowa sai kai," kai ne uwarta kaine ubanta domin zan tafi na barta acikin lisafi na kurciya Muhammad ka rike zumunci ,mukarama amana ce a hannunka ina son ka kaunaceta fiyye da komai ka kula da maraicinta da rayuwarta karka bari ta zubda hawayenta akan damuwa kowace iri ce .. duk sanda mahaifiyarsu ta tasa shi gaba tana bar masa wasiyya ya kan share hawaye yace "ki daina furta wannan kalmar inna cuta ba mutuwa ba,sannan ba'a san inda rai yake ba, babu wanda yasan gawar fari ban da Allah, baki sani ba ko mune zamu rigaki mutuwa. "kayya d'an nan dayake hk take kiransa kasancewarsa d'an fari , "wannan ciwon bana tashi bane, ni kaina ban sa ran zan warke ba har in tashi ba, domin wannan ciwon bai kamani da wasa ba, ni dai fatana ko na tafi na barku ka rike 'yar'uwarka da daraja kada ka auri macen da zata shiga tsakaninku, duk abinda, zata maka kayi hakuri kamata uziri, ku had'e kanku ka aurar daita ga mutumin da kasan zai riketa da daraja sannan ka inganta rayuwarta da karatun addini dana boko tak'arasa mgnr tana janyo numfashi da kyar wasu zafafan hawayen tausayin ya'yanta yashiga gangarowa bisa kuncinta. haka ma duk sanda mukarama ta kunsantota mgnrta kenan "mukarama ki rike d'anuwanki, ki rufa masa asiri a duk sanda hkn takasance, ki d'auke shi matsayin uba, domin hausawa sunce babban wa uba ne, ku rike zumunci atsakaninku, duk abinda kika samu nashi ne hk shima, ku zamo tsintsiya mad'aurinku daya Allah yayi muku albarka. tunda inna ta kwanta ciwo bakinta baya shr da barwa mahmamud da mukarama wasiyya da amanar junansu ,su rike junansu , ciwon dai na ajali ne rana daya zazzabin ya tashi zanga zanga suka nufi asibiti Daita ,akan hanya kmr ko wani lokaci Allah ya amshi rayuwarta batare dataga auren ya'yanta ba. bayan rasuwar mahaifiyarsu sun shiga damuwa kwarai da gaske kar ma dai mahamud yaji labari musamman idan yaga mukarama tana yawon kukan mutuwar innarsu ,duk sai tausayinta ya kamashi domin yasan dole kewar inna ta dameta, wani lokacin da kansa yake bata umarnin tashiga gidan mukotansu gurin hajara . hajara kawar mukarama ce tare suka taso tun innarsu tana da rai, basa rabuwa tare suke al'amurasu tare sukayi makarantar boko haka islamiyya ,idan bakaga mukarama ba tana gurin hajara akwai sabo da shakuwa mai tsananin atsakaninsu dama kuma can iyayensu aminan juna ne, byn rasuwar mahaifinyarsu, mahaifin hajara na d'aya daga cikin wanda ya taimakawa rayuwarsu dan haka shima mahamud lokacin daya samu rufin asiri bai manta dasu ba hatta karatu hajara shi yake biya musu kudi tare da kanwarsa ,komai ya tashi yiwa mukarama ya kan had'a da hajara yayi musu tare irin karar dayake musu , yasa iyayen hajara suke matukar jin dadi sosai, kullun cikin yabonsa suke. wata rana mahamud na gida yana wanke mashin dinsa sai kuwa hajara tashigo gidan da gudu tana huci ,sauran kiris tayi karo da machine dinsa, ganin mahamad tsaye yana kallonta sai tayi saurin komawa da wani gudun a kunyace ,ya kwalla mata Kira ta dawo da baya yace "zo nan sai kin gaya min dalilin gudun naki, bana hanaku irin wannan guge gujen ba, hajara tasa hannuwanta duka ta rufe fuskarta dashi tana dariya shima diriyar yayi kana yace "wai hajara in tambayeki shin me yasa kike jin kunyata ne? tayi shiru kanta a sunkuye yace "ko nayi miki kama da surukinki ne? nan ma shr tayi yace "ni na lura duk sanda kika shigo gidan nan bakya sakewa ko kuma tsorona kike ji.? hajara ta girgiza kai yace "to me yasa bakya iya kar'bar abu agurina sai dai mukarama ta kar'ba muku? nan ma shiru tayi mukarama ce ta fito daga cikin d'akin tana dry,mahamud ya kalli mukarama, sannan yace"wai me ya sa kawarki take jin kunyata? mukarama tace "inajin kodan taji goggo tace.... ya d'an dubeta da sauri yace "me goggon tace ? mukarama tayi shr tana kallon hajara tana dry kuma taki k'arasawa, dayake yasan halin shirmensu kurun sai ya rabu dasu yace "ku wuce kubani guri Allah yasa na sake ganin kuna irin wannan guje gujen sai kace wasu kanan nan yara. ranar wata litinin da safe mahamud yashiga gidansu hajara domin ya gaida su, hajara najin muryarsa taki fitowa daga cikin d'akin, byn sun gama gaisawa da mutanen gidan baban hajara yace"wai shin mahamud kai har yanzu baka fara tunanin aure ba ne? tunda Allah ya amshi ran mahaifiyarku ,ai sai ka d'aure ka nemi abokiyar zama kodan ka ragewa 'yaruwarka kewar innarku data rasa. yace "wallahi baba nima nayi wannan tunanin to sai dai ina kan dudubawa in samo wacce ta mallaki kanta, baba yace "naso ace ina da 'ya babba da zan kulla zumunta atsakaninmu amman tunda banida ita ga hajara nan na baka, sai a wanketa akai maka. abin yabawa mahamud mamaki ya danyi driya kana yace "lallai baba kanason ka had'a rigima kasan kuwa yadda hajara take tsananin jin tsorona ? bama haka ba baba yaushe za'a ce za'a yiwa hajara aure yarinyar da sai ma yanzu zasu kare primary, nima kuma dakake ganina karatu zan koma. mahaifin hajara yayi dry sannan yace" duk wannan bawani abu bane in dai kana sonta tunda kana son bokon itama sai ka barta tayi karatu agidanka. mahamud ya sake yin dry"amman baba baka ganin irin shirmen da zasu ta min acikin gida. "duk babu komai sai ka jure har zuwa lokacin da zasu yi hankali mahamud ya d'an dubi babar hajara yace "kin dai ji goggo ,baba yana neman ya had'ani da rigima. cikin murmushi tace "to idan haka ne ai nice na fara furtawa kai dai tunda ance anbaka ba sai kayi fatan alkhairi Allah ya tayaka riko ba, babu yadda mahamud ya iya dan haka yace shikenan goggo na karba Allah ya rika min . a daidai wannan lokacin mahamud yasamu gurbin karatu a jamiar d'an fodio dake jahar sokoto inda zai karanci kasuwanci. zance aurensa kuwa da hajara abu kmr wasa, abu ya kankama yana da shekara biyu a jimi'a aka soma shirye shiryen aure cikin kankanin lokaci aka saka hajara lalle agama biki aka kaiwa mahamud amaryarsa . ba k'aramin raino mahamud yayi ba ,kafin hajara ta zama cikakkiyar mace ba, ya dai sha shirmensu ita da mukarama, haka nan ya dage da kyautata musu kullun yana tsaye akansu komai suke bukata zai siyo ya kawo musu da yake yara ne masu hankali da natsuwa sukayi zamansu lafiya su fad'i tare su tashi tare suna harkarsu su duka suna jin dadi zama da junansu ahankali ahankali rayuwarsu ta cigaba da gudana cikin jin dadi har sanda mukarama tasamu karatu a makaranta kwana dake aleiro government girl's comprehensive secondary school aleiro, yayinda hajara kuma ya samammata makaranta anan cikin garinsu, dan Allah ya tallafisu ya amshi rokonsu yasa aka bud'e musu jeka ka dawo. kullun zata makaranta idan ta tashi ta dawo gidan mijinta, tayi girki da sauransu hidimomi gida, rayuwarsu dai gwanin sha'awa in kaga yadda mahamud yake tattalin hajara sai ka rantse wata shararriya soyayya sukayi kafin aurensu. shi dai mahamud mutun ne mai son mace taji dadi gashi da busha sha, ga sakin fuska da saukin kai ,hajara dai ta samu soyayya da kulawa agurin mijinta, kullun babanta na saka masa albakar saboda ya rike amanar da'aka bashi kuma gashi da zumunci domin mahamud ya maida iyayen hajara tamkar nasa komai zaiyi ya kan nemi shawararsu haka suka cigaba da rayuwa ganin sha'awa . ta bangarensa karatunsa ma bashi da wata matsala komai na tafiyar masa yadda yakamata idan ya dawo hutu kuwa zai kama kasuwancinsa na siye da siyar, sannan ya bud'e k'aramin shago a kofar gidansu wanda yake gyara agogo. ****** lokaci zuwa lokaci idan mukarama tazo hutu hk samari ke yi mata caaaa amman sam mahamud ya kekashe kasa yace "bai san da wannan zance ba, karatu zatayi duk wanda yaji zai iya jiranta to ya jira ,wanda ba zai iya ba, ya k'ara gaba ya nemi matarsa, cikin haka ya kammala da karatunsa ,kasuwancinsa ya k'ara bukasa, komai yana gara masa domin zuwa yanzu ya fantsana cikin duniya neman arziki, dan har sun bar kauyensu zuwa cikin birnin ilorin state . byn wani kankanin lokaci sai gashi ya zama matashi attajiri dake da mallakin gidaje, ya sayi motaci baya ga yaran kauyensu daya Diba suke karkashinsa. zuwa lokacin yana da yaro daya mai sunan Ibrahim ,suna kiransa da akram da yake sunan mahaifinsa garesa .. mukarama ta tagama karatunta na gaba da primary, ta zama cikakkiyar budurwa sosai gata da kyau da gogewa da iya tsara kwalliya ,cikin wannan lokacin ishaq abokin Muhammad wanda ya kasance abokin kasuwancinsa ne ya dawo daga kasar maleshia akan harkan kasuwanci da karatunsa . ishaq hadadden matashi saurayi ne tsayaye mai zati da haiba uwa uba naira ta zauna ajikinsa asalinsa dan Kano ne amman babu inda baya shiga adalilin kasuwanci. wata rana ya kawowa Muhammad ziyara,inda Muhammad yace "mukarama ta kawowa abokinsa abun motsa baki,tashigo parlour'n cike da natsuwa da kamewa uwa uba kunya, ai kuwa ishaq yana d'aura idanunsa akanta yarasa tsukuni amman dayayi wani tunani sai yayi saurin kawar da abinda yaji akanta, ta ajiye tire ishaq yace "ga leda nan ta wuce dashi tsarabarsu ce aciki, sam mukarama taki d'auka, ya d'auka ya mika mata nan ma taki amsa yace" haba kanwarmu ina ganinki mai kalar wayyayu, a wannan zamanin yaushe ake kunya hk? mukarama ta juya akunyace zata fice daga parlour'n, 'yar drya Muhammad yayi yace "to in kin shiga ki turomin hajara kawai ,tana fita ishaq yace "amman wannan wani irin kunya ce hk sai kace ba yar zamani ba? alhj Muhammad yace" ina ruwan mukarama haka Allah yayita komai nata sai ta had'a da kunya yarinya ce mai tsananin kawaici babu ruwanta. yace "da kyau hk nake son naga mace nada kawaici da alkunya a dukkanin al'amuranta da ganin kanwar tamu mijinta ya dace kwarai ya fad'i hk saboda tunaninsa ko tana da aure. alhj Muhammad yace"kuma ka gani bata da miji har yanzu bata tsaida miji ba karatu take domin ina da burin akanta,ina son na ingata rayuwarta da karatu boko domin a dama wannan duniyar daita, shiyasa duk masu kawo hari nake katse masu hanzari har sai ta gama, yanzu haka tana matakin diploma . ishaq ya d'an dubesa a razane domin yasan asaninsa mutane karkara haka ,basu fiyye barin yaransu su jima hk batare da yin aure ba .... "gsky abokina kayi nmj k'ok'arin gurin ingata rayuwarta ,yanzu dai kace babu kowa akasa masu neman aurenta? "babu kowa ina suka ga fuska, ai sai sunga fuska tukun zasu zo, ni dai burina tayi karatu mai zurfi ta yadda zata taimaki al'umma da ita kanta, nan dai suka bar zance suka shiga hirar kasuwanci dayake daman harkar kasuwamci ne ta had'asu har suka zama abokai, acikinsu duk wanda wata harka tashigo hannunsa daya san za'a samu alheri y kan janyo dan'uwansa ciki, su samu alkhairi tare kasancewar dukansu ba masu kyashi ko bakinciki bane ,kowa yana k'aruwa da kowa suna harkar arziki tare gwanin sha'awa. tunda ishaq yakoma gida sai ya kasa samun sukunin zuciya duk yadda ya runtse idanunsa mukarama yake gani tana yi masa gizo ,haka nan abin mamaki jiyayi gbdy ya tsinci kanshi da matsanancin kaunar mukarama ,ganin dayayi mata ya gigita kwalkwaluwarsa ,sosai yarinyar ta rikitashi ,ya rikice akanta har tunaninta na neman hanashi sukuni yin barci, shi kansa sai juya al'amarin yake aransa yadda farat daya ya gigice akanta gashi dan'uwanta na da buri akanta, dan hk ya danne abun aransa yacigaba da hakuri ,haka soyayar mukarama yayita cinsa arai har sai da aka samu wasu yan watani. ************ ran nan dai ishaq ya kasa hakuri adalilin soyayyar mukarama da kullun take sake huda kahon zuciyarsa, dan hk a zaunen da yake agaban mahamud yasoma maganar yadda yake son mukarama. mahamud yayi shr yana sauraron abokinsa har yagama zayyana masa irin kaunar dayake yiwa mukarama,Muhammad yace "naji dadi kwarai kuma ina matukar farinciki da wannan bayani naka ,sanin kanka ne kafi karfin komai agurina ,zai yi wuya ka nemi wani abu a wurina na hanaka, musamman ma irin wannan alfarma ta aure, to amman akwai wani hanzari ba gudu ba kmr yadda kasani, bazan aurawa mukarama mijin da bazai barta tacigaba da karatunta ba, matsawar ka amince zata cigaba da karatunta agidanka shikenan na amince kaje ka nemi yardarta matukar ta amince da kai zan aura maka ita. ishaq ya sauke naunauyen ajiyar zuciya kana yace "wannan ba wata matsala bace ni kaina har yanzu akan karatu nake kasan da haka ,domin lamarin kasuwancinmu na bukatar ilimi mai zurfi,bugu da kari ilimin mace nada matukar mahimmanci arayuwa. "haka ne kam Allah yasa mu dace kana iya turo magabatanka idan ta amince , ishaq yace "ameen had'e dayiwa abokinsa godiya " domin sosai yaji dadin lafazinsa mahamud na gama fadar hk ya bari parlour'n. ishaq ya nemi ganawa da mukarama ,byn tashigo parlour'n suka dan yi shru kad'an sannan yakira sunanta "ko kinsan zuwan nawa na yau dominki ne sabanin sauran lokuta? ta d'an kalleshi cikin natsuwa, yayinda ta zuba masa idanu tana kallonsa da sauraren abinda zaice dan gabad'aya zuciyarta ta matsu da son jin abinda ke cin ransa akanta, domin itama tana jin wani abu a game dashi . yacigaba "hakika mukarama dazaki min alfamar dana dan gutsara miki abinda ke cin raina a game dake, Allah yasamin tsananin kaunarki tun ranar farko dana d'aura idanuna akanki dayake nasan ba aure yayanki zai miki a wannan lokacin ba sai nayi kokarin danne sonki cikin zuciyata har sai yanxu ,a yanzu dai ina gabatar miki da kaina amatsayin wanda yake son aurenki amman menene ra'ayinki akaina ? mukarama dai tayi shiru saboda batasan amsar dazata bashi ba, domin mutumin yana yi mata kwarjini ganin bata da niyyar bashi amsa yace "haba mukarama ya kikayi shr ai gara kiyi magana shi sha'anin aure ai ba'a yinsa da wasa zan so jin ta bakinki koda bakya sona barema bana fatan haka nafi son kiyi min alfarma bisa soyayya kar ma ki tsaya duba alaka don ba itace tasani sonki ba. " kyawawan halaiyenki da dabi'unki na kirki ne suka janyo zazzafar kaunarki ,ki taimawa rayuwar wannan tsohon tuxuron ki aureshi domin idan kika ki aurensa ina tabbatar miki hk zai k'arasa sauran rayuwarsa batare daya ajiye iyali ba. mukarama ta cigaba da yin shiru sai dai wannan karon kanta na sunkuye ,murmushi yayi saboda sanin halinta na kunya "haba zuciyar ishaq ki dan yi min magana ko naji dadi "tayi dariya amman batace komai ba yace"kenan dai ana son ishaq ya hakura," mai yiwuwa ina da wani abun da baza a soni dominsa ba? sai a lokacin ta girgiza kanta, yace "ni kam muddin ba magana ki kai ba, gani nake ban canci asoni ba ,shi yasa kika barni da kokon barana a hannu, ai sauran maneman ba hk ake musu ba, ko kuma ko dan anga ni babban yaya ne kike ganin nayi miki tsufa? maganarsa ta bata dariya har ta sa ta d'ago kanta da sauri suka dubi juna sannan tace "ko kad'an ba haka bane, ni dai aguna baka da wani aibu da kowace irin mace zata kika ,sai dai abunda nake son kagane ban taba yankewa kaina hukunci ba sai dai yayana ya yanke min. "idan ta wannan bangare ne mugama magana da yayanki har ya amince har ma da sharadinsa nason ki cigaba da karatunki byn aurenmu, na kuma ji na gani na amince da hakan ,saboda ina matsanamcin sonki "duk da haka ni dai nayiwa kaina alkwarin komai zanyi sai da amincewarsa. "da kyau kinga wannan biyayyar taki tana daga cikin abubuwan dayasa na kamu da sonki tunda kin tabbatar zabin d'anuwanki shine zabinki, a she dai naci babu hamayya kenan, domin na tabbatar d'anuwanki ba zai iya zaba miki wani fiyye dani ba. "amman duk da hk xan baki lokaci kije kuyi shawara da matar yayanki tunda itace ta hannun damarki, dan ta abokina shi bana jin komai domin shine yace in nemi soyayya agurinki domin yana son baki cikakkiyar yanci shiyasa nake ganin yanzu shawara ta rage keda hajara babu ruwan aminina ,dan ko yau muka daidaita gobe ma yana iya d'aura mana aure. ta dan fad'ad'a murmushinta "shikenan Allah yayi mana zabi mafi alkhari "yauwa masoyayyita abinda nake son ji kenan daga gareki, domin zabin Allah shine mafi alkhairi a gurinmu, gbdy dai ishaq ya gama kashewa mukarama jiki da salon soyayyarsa wanda sukayi tasiri a zuciyarta. sosai yasamu matsugunni agurinta ,byn sunyi sallama tare da yi mata alkwarin zai dawo wani sati domin jin shawarar data yanke, kafin su rabu sai da yayi mata alkhairi mai yawa wanda kunya ta hanata kar'ba ,sai daya takurata sosai sannan ta amsa game da yi masa godiya tashige ciki, tana shiga Kai tsaye d'akin hajara tashiga domin ta fesa mata labari da bata ganta cikin parlour'n ba sai ta bita uwar daka ta isketa kwance ita da akram akan lafiyayyen gadonta suna ta sharar bacci cikin nishadi ta dan ja ta tsaya tana jan tsaki . "ke kam aunty hajara kin cika so baccin tsiya ta fad'i hkn a fii yayinda tasa hannu tana girgizata, ta d'an motsa kadan tare da rungume d'anta ajikinta batare da ta bud'e idanunta ba ta sake komawa bacci abinta . a hanzarce mukarama ta maka mata duka, hajara a firgice ta d'an bud'e idanunta ganin mukaramaa tsaye akansu tace "kai d'an Allah mukarama in banda d'aukar haki ki barmu muyi baccinmu . mukarama cikin zolaya tace "mijinki yace na taimaka na tasheki sai nayi laifi? hajara da sauri ta watseke tare da tashi, zaune har da d'an murmushinta, mukarama ta kwashe da dry "uhm yar dadi miji daga jin zance miji kin wani wartsetake to karya ne bashine yake nemanki ba ni nake son mgn dake hajara ta d'an kai mata duka "kyaji da karyarki ke daman babu damar kiga mutun yayi bacci sai kin tasheshi . mukarama tace "ai ina ganin akan shegen baccin nan naki sai nayi miki kishiya in tura amarya d'akin yayana kina nan kina shirgar bacci. "haba dan Allah kin isa ai dagani babu kari ai ni nafi karfin amarya. "kiyi cika bakinki kigama zanyi maganinki . suka fashe da drya . kiyi driyarki ahankali karki tasar min da yaro inji cewar mukarama. "ai kuwa babu mai hanani magana, kiyi shru albishir nazo miki kinsamu dankareren suruki idan bakiyi shiru ba wallahi na fasa "hajara tazaro ido "da gaske koda wasa "da gaske mana "to waye surukin nawa? "abokin yaya. hajara tayi dry har da shewa "gsky in dai shine yayi min, mukarama ta zauna ta zayyene mata yada sukayi sai data gama jin komai tayi murmushi tace "haba ai daman nasan za'a rina shiyasa kika ga ko mamaki banyi ba kinsa ance inkaga kare yana shinshina takalmi d'auka yake son yi ,Allah dai ya tabbatar da alkhari gsky kinyi sa'a more miji d'an gayu d'an boko attajiri kyakkwawa... "kinga ba surutu nace ki min ba shawara nazo kibani "hajara tace kawai ki auri abunki tunda mu duk muna sonshi ba wata matsala kuma bashi da wani aibu dan ko mutumin kirki ne gashi attajiri in kika aureshi zakiji dadi mukarama tace"ki ture zance kudi kinsan ni kudi basu dameni ba, ni kawai kwanciyar hankali nake nema atare da namiji. "karki damu in dai kina sonshi kurum ki aureshi ni dai ina baki goyon baya karma ki tsaya wani hasashe kiyi aurenki kawai da zuciya daya ki shiga gidansa da kyakkyawar niyya Allah ne mai bada zaman lfy bare ma nasan mutumin Nada kirki, zai rikeki amana. mukarama tace" shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi in yaya yashigo ki gaya masa na amince hajara tayi dry shikenan ishaq zai d'auke mana ke ,zamuyi kewarki in kin tafi dawa zamuyi hira? sai ki dinga yi da mijinki, ni meye zai dameni tunda nasamu nawa abokin hirar. hajara tace "dadin abun dai baki da baki balle nasa ran zaki yi hira da miji "ki kwantar da hankalinki wannan karon zaki sha mamaki yadda bakina zai bud'e bari dai ayi auren ,ni nasan irin soyayyar da zan nunawa ishaq ,ke ko fita sai naga dama zan barshi suka kyalkyale da dry gabad'aya hajaa tace "kmr gaske "a ture maganar wasa zan dinga tarairayarsa domim karya hango wata. hajarra tace "ai shi nmj bakomai bane idan yashiga hannun mace mai wayo, komai girmansa ya kan dawo tmkr yaro in har ya had'u da macen da ta iya kissa sannan ladabi da biyayya ma wani ginshiki ne a cikin zaman aure, amman mu mata hausawa duk bama d'aukar wad'an nan abubuwan da mahimmanci . mukarama tace "ai kuwa duk kina yi babu laifi kina k'ok'arin kamantawa gashi nan kullun sai k'ara rikita min yayana kike abun bako tausayi "kema ba gashi nan kina shirin zuwa ki rikita yayan wasu ba " amman ai kinsa ni nafiki kunya bazan dinga irin abinda kike yiwa yayana ba. "zauna nan garin jin kunya a je ayi bake, gara ma in zaki cire kunya tun wuri ki cire domin mazan zamani nan basu wani so kunyar nan, ki zage ki tarairayi mijinki, "yanxu ina karuwai suke a gari? "babu su domin karuwai na d'akin mazajensu, wallahi wata idan kikaga iskancin datake zubawa mijinta domin gamsar dashi sai kinyi mamaki ,yanzu karuwai babu market kowace takama gabanta.. suka fashe da drya a daidai lokacin da Muhammad yashigo ya daga labule d'akin "to gwana kingama mata hudubar? kunya duk takama mukarama a zuciyarta tace" Allah dai yasa ba duka hirarsu yaji ba hajara kuwa ta dake tace "kai kace daman la'be kake mana ,ka dai san la'be babu kyau. cikin driya yace "ina ruwana da hirar shirmenku, ke din ma yaushe kikayi baki har da zaki koyawa wata yadda zata rikita miji ya zauna a tafin hannuta? mukarama tayi saurin cewa "kai yaya bafa hk tace min ba, zancemu ne kurun mukeyi ,"idan haka yaji sai me kissa nake koya miki don abokinsa yazamo a tafin hannunki Muhammad ya dube yana yar dariya "ke din me kika iya balle har ki koyawa wata? ta d'an hararesa "haka din da kake rainawa dai ina yi ma ,ina laifi ma da kasamu hk wasu mazan nacan basu samu irin kulawar da nake maka ba. ganin mukarama na gurin yasa yayi saurin wayancewa "karki sake yarda da hudubar wannan kawartaki mallake nmj a tafin hannunki bashine ba ladabi da biyayya shine gaba da komai ,halaiyar kirki ake neman ga mace. hajara tace "da kuma me ? yace "da iya girki ta sake cewa byn nan fa? tana kallonsa tana dry "ke mukarama ina ganin , in dai abokina yayi miki shikenan sai ayi magana aure kin dai san ba gurin da za'a tsaya 'bata lokacin bane , in kuma ba kya sonsa gara tun wuri ki gaya min in sanar dashi domin babu wata yaudara atsakaninmu dashi, ko ban fad'a miki ba Kinsa matsayinsa agurina, in kina sonsa komai cikin gaugawa za'a yi agama ba tsayawa za'a yi ana ja masa rai ba ,kinsa ni ban iya kwalo kwalo ba ya fad'a yana kallon mukarama wace tace "yaya ai magana tana hanunka sai abinda kace, ni duk abinda ka yanke daidai ne. girgiza kai yayi "haba mukarama ki dai ki fad'i son zuciyarki idan kina so nima ina so, idan kuwa baki so nima banaso "ai ni matsawar kana da rai bazan iya yankewa kaina hukunci ba, sai abinda ka yanke min,. ya d'an yi shiru hajara tace "tunda hk ne shikenan aje mun zabi abokinka sai kace ya fito ya d'an washe baki yana murmushin jin dadi "lallai kun kyauta min kuma mukarama ta fiddani kunya in ta aureshi zan fi kowa farinciki saboda abokina mutumin kirki ne nasan bazaki ta'ba nadamar aurensa ba, nagode Allah yayi miki albarka bisa biyayyar da kike min.. mmn sudais ce [12/19, 11:01 PM] +234 806 956 2358: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU AYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ WARNING!!! FOR THE FIRST TIME !!!! I WILL LIKE TO SAY," DON'TS READ THIS NOVEL ,IF YOU KNOW YOU ARE NOT MARRIED... ❌❌❌COZ THIS BOOK CONTAINS ONLY FOR MATURE PEOPLE , IF YOU READ IT, IS FOR YOUR OWN RISK ...... WATTPAD @HAUESH BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM Page 3 ......Tun da alhj Mahamud yasoma sanyawa mukarama albarka ,murmushi yaki 'bacewa a fuskarta ,hajara ta du'beta a sukwane tace "kai duniya mukarama ko kunya baki ji ,ana zance aurenki kina guri , sai wani nishad'i da annashuwa kikeyi .. Wani sabon murmushi mukarama ta sake yi "bil hakki da gaske mugun son ishaq ya kamata sosai tun kwanaki ma na lura da rawar kafar da takeyi akansa ,kalli ma yanzu kaga rawar jikin da take ,barin in taji yazo gidan ta dinga 'bare 'bare kenan tana hanzari zuwa gaidashi ,wata sabuwar kunya ta kama mukarama ta tashi da sauri zata fice daga d'akin tana dariya ,alhj Mahmoud ya dakatar daita "kinga dawo kiyi zamanki in dai tsiyar hajara ce kin saba daita ,tunda tayi baki neman take ta bud'e bakin kowa ta karfi da yaji. Mukarama tace 'kai ma yaya kayi mata kishiya kawai mu huta da halinta hajara ta kwashe da dariya ahayyeeeeee yau zan ga had'in kai acikin gidan nan, to Dan kince yayi min amarya sai me ? Ince ba'a kaina aka fara ba sannan kuma ba akaina zata zauna ba ita shegiyar kishiyar, tazo Dan ubanta ... "Duk dadin baki yayanki yake miki Dan yaga zaki yi auri abokinsa yanzu da wani ne da watakilla ya rungumi transformer Amman shi Da kansa yasan mijin mace daya ne .. Alhj Mahmoud yace " yarinya karki cika baki in kika zugani gobe gobe sai ,naje na biya sadakin wata yarinya da take mutuwar sona in ga tsiya" Mukarama ta kwashe da dariya, har da yiwa hajara gwalo, hajara tace" lallai mukarama wai ni kike kwayewa baya agaban yayanki bari ? "La yaya kalli kaga daga jin zancen kishiya har idanun hajara ya raina fata ..sukayi Dariya gabadayansu har hajara wace cikin dariya tace "zan miki mummunar addu'a kema kina shiga gidan ahmed da wata biyu ya gano wata ,tunda dai zuga shi kike yi ayi min kishiya ,wace Sam sunanta ma bai da dadin fad'a . ******* Byn Sati biyu ishaq ya sake zuwa gurin mukarama byn sun gaisa suka zarce da hira, wannan karon yaji dadi sosai da yadda ta sake dashi har suka tautauna sosai da kanshi yace "na ji dadin irin kar'buwar Dana samu duk da dai har yanzu baki furta min cewar kina sona ba ,Amman dai na gamsu dari bisa dari sannan na gamsu da bayyani da yayanki yayi min kuma hausawa sunce labarin zuciya a tambayi fuska ,ina ga tun da mun rigada mun amincewa juna ai ba sai an d'auki dogon lokaci ba ,abin nan tuwona maina ne zan so ace mun yanke lokaci kinga tun daga yanzu mu fara shirye shirye Dan tun Dana sheidawa hjyta batunki ta kasa zaune ta kasa tsaye, domin burinta arayuwa bai wuce taga na ajiye iyali ba Amman me kika gani? Ta D'an dubeshi cikin murmushi tace "ina ganin wannan maganar zaifi kyau kuyita tsakaninka da yayana "eh na San da haka ,Amman shi Mahmood ya sheida min, in dai ina bukatar aurenki ko gobe ma zai iya d'aura mana aure ,shi yasa nake ganin nida ke yakamata mu zauna mu tsara lokacin da muke bukata . Ta janyo ajiyar zuciya da kyar ta fesar saboda yadda maganarsa ke shiga jikinta kana tace " to kai kmr wani lokaci kake ganin ya dace ? "Yauwa zuciyar ishaq ni dai idan kin amince zuwa karshen shekarar nan yayi min ,nan da wata biyu kenan sai ayi komai cikin gaugawa a d'aura aure tare da biki, ta D'an fad'ad'a murmushinta tana kallonshi tmkr yau ce rana ta farko data soma sanyashi acikin idanunta . ahankali muryata ta fito still kwayar idanunta na cikin nashi tace "haba dai nan da wata biyu ina ma laifin wata uku . Yayi saurin ware mata matsakaitan idanunsa ,"wani irin wata uku idan dai baso kike labarin mutuwata ta riskeki ba ,ko na dibo kayana na dawo gidanku da zama ba,ki San ko irin yadda nake jinki a zuciyata? "In aka kai watanin uku ba'a shafa fatiha ba,ai sai na fara sanbatu ,mgnr yabasu dariya gabadaya "in dai ba wani babban uzuri gareki ba ,gaskiya bana son a dau lokacin domin ina son muje aikin haji tare InshaAllahu,dan alkwari nayiwa kaina bazanje aikin hajji ba sai da matata saboda zanfi jin dadin tafiya tare da iyalina, Amman ban sani ba watani uku da kika ambata ko akwai wani tanadi na musamman da za'a yi domina ? "sai in hakura har zuwa wani lokaci kinsa ku mata bakwai rabo da daburu da hikimomi. "Ta sunkuyar da kanta kasa "babu wani shiri da zanyi daman gani nake kafin lokacin mun Dan dada fahimtar juna "ai babu wata fahimtar data wuce kaunar da take cikin zukatanmu kin Riga kin San ina sonki ,kema ko baki fad'a ba nasan kina sona batun yau ba na gane akwai kaunata a zuciyarki . A kunyace ta rufe fuskarta tana dry "kinga kuwa fahimtar juna bazata yi wahala ba ,yanzu dai kin amince min karshen watan nan nake son na turo kayan aurena kuma in kin tashi tarewa banason yayanki yayi wahalar siyan komai domin babu abinda ban zuba acikin sabon gidana ba ,komai akwai ke kawai suke jira . Cikin murmushi tace "bakasan yadda yaya ya fika d'aukin wannan auren ba ,domin tunda yaji ka furta maganar auren yayi oder a kamfan, hatta kayan kitchen ya gama siya .. Ishaq yayi D'an murmushi "ina ruwan mutumina ai naga alamar yafi kowa doki auren nan, to tun da yake ya rigada ya siya miki kayan d'aki babu komai asasu a extara room's. kanta a sunkuye tace "shikenan Allah ya nuna mana ya kara budi Amman ni dai Dan Allah karkace zakayi wata hidima kayan aure komai na yafe, ya D'an dubeta cike da fara'a a zahiri gsky yaji dadin kalamanta "GSKY sai dai kiyi hakuri Dan koni bance zanyi ba dole dangina suyi bare kuma allah ya horemun abinda zan miki dole nayi komai da'akewa matashiyar budurwa kmr ki, kisawa ranki duk abinda ake yi na hidimar aure zan miki ,ni ko banason mace zanyi mata hidimar aure balle ke da zuciyata take kwakwa tayi murmushi "to ai ni nace na yafe ko? Cikin murmushi ya tsura mata ido yana dubanta salon maganarta da komai na Burgesa "zuciyar ishaq ya fad'a yana sake tsareta da idanunsa "ki duba kanki da kyau ,kiga irin baiwar halittar da Allah yayi miki ai jikinki ya wuce irin macen dazatace ta yafe kayan aure ,kuma ya yafu din. Ta rufe fuskarta tana dry saboda kunya "dadina dake kin fiyye kunya da yawa wallahi yanzu haka zamuyi zaman aure kina jin kunyata? "Kayi hakuri zan D'an rage in naje gidanka "gsky yakamata Dan nasoma jin tsoron wannan kunyar Dan hka tun daga waje yakamata ki soma ragewa kinga idan na kaiki gidana na zamo abokin rayuwarki, kinga maganar kunya ma bata taso ba ,kunyar nan ki kawar daita domin mu had'u mu ingata rayuwar aurenmu. " ni zama abokin wasanki ,abokin nishadinki, abokin Hirarki ,abokin barkwancinki ,kinga ni mutun ne mai son nishadi don hk nake bukatar cire wannan kunyar ,ko tun yanzu ni na cireta da kaina ya kai hannunsa zai ta 'bata tayi saurin dojewa da sauri zuciyarta na bugawa domin tunda taso arayuwata babu nmj daya ta'ba d'aura hannunsa ajikinta "babu abinda zan miki ,domin Sam bakiyi kama da tsagairan mata ba ,akwai cikar Kamala atare dake ,hankalinki da tunaninki tare da natsuwarki yasa nake kyautata kyakkyawan zato acikin rayuwar aurenmu ,Dan haka ina fatan zaki cire kunyar nan kiyi masa babban ma'aji agidan yayanki domin ishaq a yunwace yake dake ,ba zai iya da wannan kunyar ba "ki yi min akwarin cire kunyar ko na soma cirewa da kaina ? Muryarta a matukar sanyaye tace "karkaji komai nayi maka alkwarin InshaAllahu zan cire ,tun yanxu ma na fara cirewa ...duk yadda taso kauce masa sai daya matsota sosai tmkr zai shige jikinta yana narke mata har yayi nasarar kamo fuskarta ya daidaita da nashi suna shakar numfashin juna .. Wata irin soyayya ishaq yake nuna wa mukarama mai tsuma zuciya sai dai duk yadda yaso ya dinga romancing dinta taki yarda ,ta dinga nuna masa hkn haramu ne ya bari har sanda zasu mallaki juna . Ishaq ya turo iyayensa aka kawo komai na aure tare da tsaida lokacin wanda bai wuce wata biyu kamar yadda ya bukata . ********** Anyi biki lafiya amarya ta tare agidan angonta ishaq ba k'aramin shirya mata gida yayi ba ,gida kmr aljannar duniya komai yaji ban da tsiya babu abinda babu acikin gidan duk wani kayan jin dadi da more rayuwa an zuba mata takowani bangare ,gidan kam sai Wanda yagani ya had'u karshen had'uwa ,kai daga ganin gidan kasan naira ta zauna ,gabadaya mukarama ta tsinke da alamarin ishaq duk da tasan wani kusan attajiri ne ,Amman shigowarta gidansa tasan ya taka matsayin mai girma wajen dukiya. byn 'yan kawo amarya sun watse mukarama ta sake sabuwar kwaliya saboda shirin tarbar miji duk da yadda zuciyarta ke luguden bugu, ta saka wani ratsetsen blue less ,Wanda tsayawa fad'ar kudinsa 'bata baki ne, ga zinarin da yayanta ya sai mata hannu da wuya sai sheki take irin turarrukan da tayi amfani dasu ita kanta bazata iya lisafasu ba, gabadaya gidan ya d'auki kamshi a haka ango yashigo ya sameta zaune a bakin gado lullube da mayafi ya D'an sa hannu ya yaye mayafin data rufe jikinta dashi yana mata dry. Tsura mata kyawawan idanunsa yayi yana kallonta hk nan yaji amarya tasa tafi kowace mace kyau a duniya yasan gwanar Ado ce Amman na yau yafita daban kodan ya had'e Dana amarci ne, bai sani ba ,kallonta yake yana kallon halittar Allah irin kallon kurulla ,sai ta D'an sunkuyar da kanta tana murmushi habarta ya d'ago yasanya kwayar idanunsa cikin sannan yace "zuciyar ishaq duk yadda akayi kinyi kuka ko? Ta D'an dubeshi kawai kana tace "me kagani ? "Naga idanunki sun canza sunyi ja, kin tuna wani abu daya Sosa miki zuciya ne ? Tayi murmushin tana neman wayancewa ,in har ta sanar dashi dalilin kukanta zatayi tace mishi me ? Kmr yashiga zuciyarta yace "kiyi hakuri zuciyata ko baki fad'a ba ni nasan abu daya zai iya sakaki kuka a irin wannan lokacin bai wuce kin tuna da innarki ba, musamman idan mace tayi auren fari Amman ki kwantar da hankalinki ishaq zai rikieki amana, zai zame miki komai ,kani yaya dangi da komai nayi alkwarin kyautata miki InshaAllahu, daga yau bazaki sake kukan mutuwarta ba, komai runtsi zanyi k'ok'arin sanyaya miki zuciya ,zan rikeki amana zan kula da maraicinki, zan kyautata miki, San jiyar dake dadin dake cikin duniya gwargwadon ikona, zan soki, zan kaunaceki, Zan faranta miki bazaki ta'ba nadamar aurena ba, ta 'dan murmusa cike da jin dadin kalamansa sannan tace "nagode da alkwarin daka d'auka zan tayaka da addua Allah yabaka iko sauke nauyi dake kanka "amen. Ka fad'i komai bakayi mgn akan cigaban karatuna da yayana ya kwallafa rai akansa ba ...ya tsinkayi muryata cikin dodon kunnenshi ya d'ago ahankali ya tsareta da ido kawai sai dry ta subuce mata aiko suka sa dariya gabadayansu ya kamo hannuta cikin nasa "ban manta ba ina sane zakiyi karatu har sai kin gaji matukar kina tare dani, domin ni kaina mai son yin karatu ne .. Yanzu kin gaji dayawa saboda hidimar biki ,a yanzu Hutu kike bukata ba zance wani karatu ba, Dan hk nake son ki biyoni muje d'akina Muje ki kwanta ki huta.. Batare da mutsu ba ta Mike ta yafa mayafinta ya d'aukar mata sabuwar rigar bacci suka fito tare da kansa ya rufo bangarenta suka fito suka nufi bangarensa suna shiga yace "ina ganin kafin bacci yakamata mu fara gabatar da sallah nafila kmr yadda Manzon rahma ya Umarci ma'auratan da suka yi sabon aure suyi ,Dan neman zaman lfy da samun zuria na gari..... Mmn sudais [12/19, 11:01 PM] +234 806 956 2358: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU AYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ warning!!! for the first time !!!! i will like to say," don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you read it, is for your own risk ...... WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim Page 4 ....Bayan sun idar da sallah,ishaq yayi mata tambayoyi akan addini,sosai yaji dadin yadda ta bashi amsar duk wata tambaya da yayi mata ,dama kuma bai yi tsammanin zata kasa amsa daya daga cikin tambayoyin da yayi mata ba. suna nan zaune akan sallayar suka zarce da hirar soyayya ,ishaq yace "ina ga kmr bacci kike ji gashi har kin soma hamma da zaki d'aure sai ki D'an ci abinci sannan sai mu kwanta "bana jin cin wani abinci yanzu, Amman dai zan d'an sha lemo bari na zuba maka abinci kaci ,da yake lokacin daza'a kawota hajara tayi musu tsarabar abinci na musamman koda baza'a kawo musu ta bangaren ishaq ba, ta tashi cikin natsuwa tana taku na Burgewa ta isa tablet ta d'auki plet Zata zuba mishi ,ya dakatar daita" karki zubo abincin nan dibo nama kawai kizo ki tayani ci nama, nima sai na tayaki shan lemo . Ta D'an kallesa tana murmushi "wai ita zai yiwa yawo, ita fa gabadaya ta gama harbo jirginsa ,d'aure kawai take dan kada ya gano tsoronta a fili ,Amman cike take da matsanancin tashin hankali da fargaba wannan daren. Ta bubbud'e ladodin naman dake wurin ,kowane ta tsukara aciki ,akwai soyayyen nama akwai balango akwai tsire ,da kaza gasashiya, duk ta kawo gabanshi ta ajiye ,kana ta tsiyaya masa ruwan tattaciyar lemu ta zauna suka fara ci dadin naman ya ratsata Amman still kirjinta na luguden bugu ,saboda irin mayayaccen kallon da yake binta dashi. ahankali muryarsa ta fito da kyar yace "zuciyar ishaq gsky kwaliyar nan taki fa tayi min kyau, "daman haka amare suke k'ara kyau ranar da suka tare a d'akin mazajensu? "Kin ji kuwa irin daddan kamshin da kike zubawa ? Mukarama ta lumshe idanunta cike da tsananin jin dadi yadda yake yaba kwaliyarta, haka nan itama daren yau wata sabuwar kaunar angon nata take jin yana ratsa kowani sashi na gangar jikinta ,dama zuciyarta ,bata da burin daya wuce ta faranta masa ,kuma bacci da gajiya da kyar zasu bari ta tarairayi mijinta,duk da ta karanto tsantsar sha'awarta acikin kwayar idanunsa. Ya ture plet din gefe ya janyota jikinsa "Anya kuwa mukarama baki gano dokinki da nake a daren yau ba ? "Wata killa da baki soma hamma da wuri ba ,domin kamshinki kawai ya isa ya rikita mutun, har yayi zaucewar ban mamaki . Tayi shiru kawai tana sauraransa gabanta na wani irin fad'uwa "Nasan abinda kikewa tunani har dayasa kikayi shiru ,sannan nasan yadda kike ji acikin zuciyarki ,kina jin wani abu mai dadi acikin zuciyarki ,kamar yadda nake ji ko? ya karasa mgnr yana mata tafiyar tsutsa a tafin kafarta da yatsun kafarsa ,Wanda take hakan yasa jikinta d'aukar rawa sakamakon haduwar da jikinsu yayi guri daya, ya kai bakinsa daidai saitin kunneta yace "kina ta hamma mukarama .... tace "in banyi hamma ba me zanyi kasan na saba da baccin wuria a gida ? "Uhmmmmm tunda hk ne gara muje mu kwanta ma k'arasa hirartamu Akan bed ,ban sani ba ko zaki bani labarin biki kafin kiyi bacci, ta D'an lumshe idanunta ta bud'e su tana kallonsa "kai ko da son hira kake tayi jarunmtar fad'ar hk.. "Gashi na ci karo da wacce batason hira ba ,Amman duk da hk sai kinyi min hira ta musamman kafin muyi bacci, idan ba haka ba ,sai dai muyi kwana zaune .. Ta narke ajikinsa sosai batare da tasan tayi hkn ba kana tace " kai Dan Allah baka tausayina? "Waya gaya miki ana jin tausayin amarya? Ta D'an murmusa kad'an idanunta a lumshe alamar bacci, ya Mike tare daita ajikinsa yana aika mata da wasu salo na musamman masu saurin rikita kwakwaluwar mutun, a duk lokacin da aka yi masa, "Muje d'aki ki kwanta Dan naga alamun bacci kikeji, suka nufi d'akin baccinsa suna mikewa tsaye ya ra'bata da jikinsa baya jin zai iya nesanta kansa daita ,tun kafin su karasa shiga d'akinsa yasoma cire kayan jikinta ,lokacin daya kawo gurin cire pent da bra , ta kamkame jikinta ajikinsa, tana fitar da numfashi da kyar. shiru yayi yana dubanta kafin daga baya ahankali ya zameta ya d'auko rigar baccin daya shigo daita ya zira mata ya d'auketa cak sai saman gadonsa ,tayi kwanciyarta tana sauke naunayen ajiyar zuciya ,gani bashi da niyyar yi mata komai yasa taji natsuwa tazo mata,yayinda shi kuma alokacin ya fara ciccire kayansa yashiga band'aki dake manne da d'akinsa ya watsa ruwa ajikinsa kana ya goge jikinsa da towel ya fito ya D'an raba ta jikinta, yana fidda numfashi mai tattare da huci ,mannota da jikinsa yayi sosai yana tsokanarta, tayi lamo ajikinsa kmr ba tajisa ba Dan batason ya lura batayi bacci ba, a zuciyarta kuwa wani irin kafirin matsanancin tsoronsa ne ke dawainiyya da ruhinta har ma da ilahirin gangar jikinta. Ahankali taji yasoma wasani da sansar jikinta tun tana jin tsoro da nauyinsa har taji komai na neman kwance mata, sakamakon jin tafin hannunsa saman nonuwanta yana shafawa tare da balle bra dinta da dayan hannunsa . Romancing din yayi sosai ,har ya nemi ya gigita, tana yunkurin yin ihu saboda yadda yake sarrafa halittar jikinta yayi saurin had'e bakinsu, Gabadaya jikinsu rawa yake ,duk wata kunya da tsoro tattare da nauyinsa da take ji sai daya tabbatar da ya kawar dasu, ya dasa tsantsar rashin jin tsoronsa da kunyarsa har ma da nauyinsa a zuciyarta sannan suka fad'a duniyar ma'aurata ,ai yana gama shigarta wasan ya canza salo ta dawo kuka da ban hakuri da neman d'auki babu Wanda bata kira ba a 'yangidansu , wayyohlly Allah yayana ,wayyohlly aunty hajara har ma da akram da bai San komai a duniya ba sai data kira sunansa, kayiwa Allah karka cire min gabana zafi nake ji, kuka take sosai tana rokonsa , Amman ishaq yaki barinta har sai daya tabbatar daya maidaita cikakkiyar mace . Bayan komai ya lafa yayi kokarin d'aga bisa kafafunta domin yin wanka ta kasa tsayuwa saboda cinyoyinta sun sage, dan haka ya cicibeta sai bayi ,yayi mata ruwan zafi yafi sau babu adadi ,yana tsokanarta, sannan yace tayi wanka tsarki ,gani ya tsaya yana kallonta yasa ta sunkuyar da kanta ya matso kusa daita sosai daidaita saitin kunneta yace "meye abun jin kunya ? "Nayi tunani na cire kunyar nan a she har yanzu da saura ,gasky ban kyautawa kaina ba . "Ni dai Dan Allah ka fita nayi wakana ,yace "to bari na juya miki baya sai kiyi ko? tayi saurin girgiza masa kai ala'mun a'a. "sai dai na fita kenan zakiyi ya tambayeta ? Ta d'aga masa kai alamun Eh, "aiko baki isa ba yarinya ,ai Dan wanka tsarki ma ba'ayiwa mutun da tuni na wankeki tassss, kinga nayi amaina na lashe kenan . babu yadda ta iya haka ta juya masa baya daga zaunen datake acikin bahun wanka tayi wanka ya sake kokarin cicibota ,ta dakatar dashi "barni kawai zan iya ,wani irin kallo yabita dashi yana tsaye yana kallonta ta fito ta barshi yana tsokanarta ,bayan ta fita yayi murmushi sannan yayi wanka shima ya fito ya raba ta jikinta ya kwanta .. Washegari ma haka yayita tsokanarta da "wayyo Allah yaya wayyohlly aunty hajara kiyo agaji zai cire min gabana ,wayyohlly akram ka ceci goggonka, atare suka sa dry gabadaya ,ya D"an duba agogon bango d'akin kana yace mata yana zuwa "zai d'an fita but yanzu zai dawo," kiyi alfarma karki daga nan ,zanje nazo da likita ta duba min ke naji har yanzu jikinki da zafi, ya juya tayi saurin kamo tafin hannunsa "plz......kawai ta iya cewa ya dawo ya rusuna agabanta ya kamo duka hannuwanta cikin nasa "plz da me kenan ? "karkazo da likita babu inda ke min ciwo ahalin yanzu ya tsareta da idanunsa "kenan zan iya k'arawa babu wata matsala? Tayi saurin fixge hannunta cikin nasa ,tana dafe kirjinta "meye hk kuma kefa kika ce kin warke ahalin yanzu babu inda ke miki ciwo? "Ni kuma daman ba koshi nayi dake ba "ni Dan Allah kabar wannan zance kar wani yajika, gaba yayi yana fad'ar kowa ma yajini matukar zaki amince ki k'aramin ai ni gaba ta kai ni.. Ko cikakken minti talatin ba'ayi ba ya dawo tare da wata likita ,byn ta duba jikin mukarama ta rubuta mata magagunna hade da yi mata allura ,tare suka fita da likitan tana yi masa bayani "babu abinda ke damunta kawai Dai sabon shiga ce a fagen , Amman wannan allurar da nayi mata da wannan maganin zai sa taji daidai a jikinta, ya ajiyeta shi kuma ya biya pharmacy ya siyo maganin ya dawo gida ya kulle gidan gabadaya saboda masu zuwa ganin d'akin amarya . Wuni ranar ishaq na gida makale da amaryarsa yana jinya ,sannan gefe daya kuma yana more kuruciyata, tare da yi mata alkwari iri iri saboda ya tambayeta abinda take so amatsayin tukuncin budurcinta data kawo masa, taki mgn sai kuka ,bayan sati daya mukarama ta warke ta daina jin zafin komai bisa k'ok'arin kulawar gawarzon mijinta ,sai dai wannan warkewar tata ta zabura da ishaq matuka inda ya dinga nuna mata salon soyayya iri iri gabadaya ya nemi ya haukata Mukarama, tun abun na bata kunya da tsoro har tazo ta daina jin komai domin dai Ishaq mutun ne mai mugun son jin dadi da son tarairaya duk inda yake yana bukatar matarsa ta kasance tare dashi, wannan abun ya haifar da shakuwa mai karfi atsakaninsu koda yaushe suna tare da juna matukar yana gida. suka zamo tamkar laila and majnun , domin dai ya koya mata irin jarabarsa sai murza amarcinsu Suke hankali kwance, babu abinda ya damesu sai soyayyar junansu, gabadaya mukarama ta tattara hankalinta wajen kula da mijinta, ida kaga yadda take tarairayarsa sai abun yabaka mamaki shima sai yayi ta narke mata sai kace wani jinjiri cikin kan'kanin lokacin mukarama ta sauya jikinta yayi kyau duk Wanda ya ganta sai ya sake dubanta . Wata irin salon soyayya take nuna masa, komai yake son tayi masa ,shi take masa batare da gajiyawa ba, Dan ita dsman Sam batasan wani abu shi gajiya ba ,ko musu ko jayyaya Akan abu ba ,kyautata da kuma biyayyar aure shine jarinta a cewarta. watansu Hud'u da aure suka lula birnin Spain honeymoon Wanda zasu d'auki shekaru kafin su dawo kasar ,yayinda acikin zuciyar ishaq yake da burin suna zuwa garin ba da jimawa ba zai samammata Gurbin karatu ,ai kuwa hakan ce takasance batare da 'bata lokaci ba ya nemmanta karatun likitanci .. ********** A Spain mukarama ta k'ara wayewa da gogewa ,idan kaganta bazaka ganeta ba ,rayuwa Suke tamkar asalin mazauna garin, kullun kuma suna makale da juna ishaq na koyar daita darasussuka na musamman mai zautar da ruhi , haka zasu had'u suyita ihun dadi acikin gidansu, Wanda zuwa yanzu babu digo daya na kunya ishaq a tattare da mukarama, ishaq yayi nasarar rabata dashi kmr yadda ya kudirta ,domin idan ba ance maka ita bace wannan mukarama ba ,bazaka sheidata ba saboda wayewar datayi uwa uba gogewa ta kowani bangare na rayuwar aure. abu d'aya ne ya kawo musu illa arayuwarsu, shine ihun da suka koyawa junansu yayin saduwa ta auratayya, suna cin juna suna ihu kamar yadda yahudawa kan yi.. Wanda wannan abun ya zama ruwan dare acikin al'umma da har yanzu muka kasa fahimtar illar abun ,ba dole sai anyi ihu yayin saduwa ba sannan za'a san ana jin dadin auratayya ba, bama gane illar abun sai mun fara tara ya'ya ,domin alokacin da kunnewan yaranmu ke jin wannan sound din na ihu da nishin dadi, shikenan bacci zai kauracewa idanunsu, a wasu lokunta ma har tsurawa iyayen idanu suke suna kallon yadda iyayensu ke saduwa da juna batare da sanin iyayen ba, abinda bamu sani ba wannan abun na zama acikin kwalkwaluwar yara sosai .. ************* tsawon shekaru uku kenan da auren mukarama da ishaq Amman har yau Allah bai albarkacesu da samun haihuwa ba sai murza marcinsu suke tamkar sabbin aure, sunyi zaryar asibitin har sun gaji Wanda zuwa lokacin har hajara ta sake haihuwar wani nmj Wanda yaci sunan mahaifinta, sai dai yaron bai Jima ba yace ga garinku .. Rashin haihuwarsu ta damu mukarama matuka saboda da har daginsa sun fara korafi akan rashin haihuwarta, dan duk lokacin da zatayi waya da daya daga cikin yan dakinsu sai sun tambayeta "kina da ciki ko har yanzu kina nan kina ci kina kasheyewa, wannan abu na masefar 'bata mata rai ,taga haihuwar nan Allah ke badawa ,ya bawa wanda yaso ya hana wanda yaso, sai a wannan alokacin ta lura da akwai wad'an basu son aurenta sosai da ishaq wanda ita batasan dalilin haka ba . a wani zuwa da ishaq yayi Nigeria ya barta a spain saboda yanayin karatunta,anan suka had'u da babbar yayarsu,aiko ta tasa shi agaba da maseefa agaban mahaifiyarsu, akan lailai sai dai ya k'ara aure, su bazasu iya zama da juya ba macen da bata haihuwa, domin dai danginsu duk masu haihuwa ne, yazo cikin dangi ya k'ara aure , ta inda take shiga bata nan take fita ba, abinda ya 'bata masa rai ,bai wuce rashin takamata burkin da hajiyarsa takiyi ,wanda hakan ya nuna masa da had'in bakinta itama tana son ya k'ara aure, cikin sanyin jiki ishaq ya baro d'akin mahaifiyarsa gabad'aya zuciyarsa ta cika da kunci ,yana son matarsa, sannan baya jin zai iya had'ata da kowa, yasan yana son haihuwa amman tunda Allah bai bashi bashi da yadda zai yi. har zuwa sanda mukarama ta kammala karatunta na likintacin Amman haihuwa shiru babu labari ,yanzu da kanta take bawa kanta kulawa da d'aura kanta akan magani ,Amman har lokacin shr kake ji ,wannan rashin haihuwa ya sake janyo mata mugun kiyayye mai karfi a gurin dagin mijinta Wanda har aka soma masa tayin yammata daban daban , Amman furrr ishaq yace "shi bashi da ra'ayin mata biyu mace daya ta isheshi rayuwar duniya kuma itace mukarama, haka suka buga suka gaji suka hakura . Mukarama ta dage da addua tana kaiwa Allah kukanta domin shine maji rokon bayinsa magani kuwa sunyi har daga Nigeria mahaifiyar ishaq take aiko musu dashi ,mukarama bata baccin daren , duk daren duniya zaka iske ko a zaune tana lazimi ko tana nafilfili, matukar ba tana tare da mijinta bane , duk karshen wata sai sunyi gwajin fitsari ko tana da ciki saboda period dinta dake canza yanayi, idan wannan watan yazo on 20 wani watan on 25 zaizo , wani watan ma sai ta shanye batayi ba sai daga baya ya zo . Allah maji rokon bawa , kwatsam sai ga mukarama da ciki har na tsawon wata biyu , murna agurin wad'an bayin Allah ba'a magana , gabadaya gigicewa sukayi har da kuka ishaq yayi Dan farinciki, ,ranar haka ya dinga rabon kudi da sadaka, ma'aikatarsa kuwa kowa ya gansa yasan yana cikin farinciki, taka nas alhj Mahmood ya d'auka iyalinsa suka zo domin taya amininsa da kuma tilon k'anwarsa murna ,cikin mukarama na girma ahankali ahankali har ya shiga wata hud'u inda tasoma jin motsin abinda ke kwance acikin cikinta . tun daga lokacin da cikin ya cika wata hudu bata sake jin motsi komai acikinta ba ,hankalinta a tashe suka nufi wani babban asibiti dake Spain, ana likitan daya dubata yake tabbatar musu da cewar ba ciki gareta ba ,mutuwar zaune sukayi agurin suna duban doctor kafin daga baya ishaq yasoma zubawa doctor ruwan bala'I "Dan mai zakace matata bata d'auke da ciki alhalin watanin baya anan hospital din aka tabbatar mana da tana dauke da ciki ? ,da kyar mukarama tasamu ta shawo kansa tana zubar da hawaye yace "tashi tashi mubar Gurin nan tun jinina bai hau ba,jiki a sanyaye ya tasata gaba suka dawo gida ranar daga ita har shi kasa runtsawa sukayi tana kuka yana rarrashi . Abu Kamar wasa zance cikin mukarama yazama tahiri,bayan sun dawo Nigeria anan aka fahimci ai cikin na nan kwantawa yayi, a inda aka tura su neman magani anan aka tabbatar musu da kwantar da ciki akayi kuma aciki daginsa mace ce tayi aikin da kitsen rakumi matukar wannan matar bata bar duniya babu yadda za'a yi mukarama ta haifi cikin jikinta sai wani ikon Allah . aiko anga tashin hankali ranar agurin ishaq, domin taka nas yayi tattaki Tun daga lagos har kano ya zabgawa daginsa rashin mutunci son rashi gabadaya matan dagin ya hada bai bar kowa ba sai matar d'an'uwansa dake zaune a London , tare da sharadin kada yaga kafar kowace shegiya daga cikin family dinsa tazo gidansa da sunan ziyara . , lokacin da suka cika shekara bakwa cikin ta takwas da aure a wannan shekarar hajara ta haifo diya mace kuma duk wannan lokacin cikin mukarama na nan sai dai baya motsi ... Farinciki agurin wannan family bai muslatatuwa, domin kuwa kowa ya kasa boye murnarsa hatta ishaq Ba'abarsa abaya ba , ita kuwa mukarama tunda tazo ganin bby taki komawa gidan mijinta, saboda wani azababben soyayyar bbyn daya shigeta, jin yarinyar take tamkar itace ta kowata duniya ,ana jibi suna alhj Mahmoud yashigo d'akin hajara bai isketa ba tana bayi tana wanka sai mukarama ya iske zaune rungume da bby tana goge hawaye. da sauri ya k'araso gareta hankalinsa a matukar tashe yana tmbyrta abinda ke sata kuka yace "ya ke ya'ruwata mai ya sakaki kuka haka ? "Hakika idan akwai abinda na tsana bai wuce ganin hawayenki ba ,banason ganinki cikin damuwa da tashin hankali ,ki fad'a min damuwarki matukar ina da yadda zanyi a yanzu zan biya miki ita . Tayi shiru taki mgn tana rungume da jariri tana kuka tana jijigata saboda kukan da takeyi kar ya tasheta a bacci "ki gaugata sanar min mukarama duk duniya baki da wanda yafini,ki fad'a min damuwarki, nine mutun na farko daya kamata yasani karki 'boye min komai "ko ishaq din ne yayi miki wani abu ? tayi saurin girgiza masa kai "to gaya min damuwarki da kyar tasoma mgn " yaya kamin alfarma ,ka tausayawa rayuwata ka ceto rayuwata daga shingi ,Nasan abinda zan tmby yana da wuyar aikatawa Amman dai dole na sanar maka tunda ka bukaci hkn "ki fad'a komaye shi matukar bai fi karfina ba zan miki " Cikin sheshekar kuka " tace "yaya wannan jaririya nake son ka mallakamin ita halak malak ta karasa mgnr tana kuka..... babu abinda ya zowa zuciyar alhj Mahmud sai maganar innarsu "ka rike mukarama amana, karka barta tayi maraici,kar abun duniya ya shiga tsakaninku, abunka nata haka itama abunta naka ne, ku rike junanku amana... hakan nan yaji hawaye ya cicciko a idanunsa ,shi ko ko zata tambayesa ya hanata wannan jaririyar ko ita kad'ai yasoma samu a duniya ai zai mallaka mata bare yana da wani kwan a duniya, ahankali taji sautin muryarsa ta ratsa cikin dodon kunneta "Dan wannan kike hasarar hawayenki mukarama ? ta kasa d'agowa haka hawaye yaki tsayuwa a idanunta. alhj Mahmud ya numfasa yace "wannan jaririyar fa ditarki ce halak malak ,bata da wata uwa duk duniya daya wuceki ,ni Mahmud na mallaka miki ita halak malak daga yanzu ba diyata bace takice sai dai ziyara Wanda bazan hana hakan faruwa ba... mukarama batasan lokacin data zube gabansa bisa gwiwowinta tana kuka mai gauraye da murmushin jin dadi ba "nagode yaya ,na gode Allah bar mana zumuncinmu, d'anuwa mai dadi, waye zai maka irin kyautar ban da d'anuwa mai zumunci irinka yaya? "ki bar kuka haka mukarama babu abinda zan mallaka kice kina so naki baki shi, AYSHA diyarki ce har abada wani farinciki yakamata sakamakon sunan innarta dataji ya furta cikin murna tace "sunan innata yaya? ya daga mata kai "sunan wa zansa mukarama? "ai daga sunanta sai naki yakamata nasa, nasa nata sai kiyi adduar nan da kwana arba'in a samu mai sunanki... sukayi murmushi "yaya ka nufin daga arba'in zan zo na tafi da muwaddat? ya d'aga kai "a'a yaya zan barta har sanda za'a yayeta sai nazo na d'auketa .. alhj mahmud yace "wannan kuma ya rage naki ,kiyi duk yadda kike so daita diya dai taki ce, fatana dai ki bata karatu kamar yadda nabaki "karkaji komai yaya karatu sai tace tagaji dashi.. hajara dake kokari fitowa daga cikin bayi kunnuwanta suka jiyo mata tautaunawarsu gabanta yayi wani irin muguwar faduwa hakan yasa ta kasa fitowa wasu zafafan hawaye suka gangaro mata ta koma ta jingina bayanta da jikin bango bayi .... Mmn sudais ce [12/23, 5:19 PM] +234 808 651 9747: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU AYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ warning!!! for the first time !!!! i will like to say," don't read this novel if you know, you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you read it, is for your own risk ...... WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim page 5 ......mukarama cike da tsantsar murna da farinciki ta tashi ta fita daga d'akin ,tana jinta sakayo daita , bata da wani sauran damuwa, ishaq ta soma kira ta sheida masa irin kyautar da akayi musu ,shi ma muranar yayi sosai . jin shirun hajara yayi yawa har kusan minti goma yana zaune bata fito daga bayi ba, yasa alhj mahmud yunkurawa ya mike daga zaunen da yake ya isa jikin kofar yana kwankwasa had'e da kiran sunanta , " hajara!!! tayi firgigib daga duniyar tunanin data lula tana goge hawayen dake kwance a kuncinta, yace "lafiya hajara har yanzu baki fito ba? da kyar ta bud'e bakinta cikin rawa murya mai nuna alamun taci kuka ta gaji tace "babu komai gani nan fitowa yanzu ,ya tura kofar yasanya kansa banda gangar jikinsa suka had'a ido daita ,kallo daya yayi mata ya fahimci tana cikin damuwa, idanuwanta sunyi jawur tamkr garwashin wuta ,da sauri ya k'arasa shiga cikin bayin ,hanunsa ya kai ya janyota suka fito tana k'ok'arin kawar da damuwarta dan kar ya gane halin da take ciki . suna gama shigowa d'akin ya rungumeta akirjinsa tsam yana shafa bayanta "nasan duk kinji abinda muka tautauna akan batun jaririya da mukarama, kuma nasa shine dalilin daya sakaki kuka ko? tayi shiru taki cewa komai sai kukan daya ci karfinta ya d'agota had'e da tsura mata ido wani irin tausayinta ne ya mamaye xuciyarsa dama gangar jikinsa, ahankali yasoma goge mata hawayen wasu na sake zubowa tasa bayan hannunta ta goge tana kallon cikin kwayar idanunsa tsawon minti goma sannan yace "kiyi hakuri bansan zakiyi kuka har ma da shiga damuwa akan na d'auki mai sunan inna na bawa mukarama ba, saboda a tunanina ko bani kika aura ba ,ke mai d'auka diyar cikinki ce ki bata saboda amintar dake tsakaninku? ahankali ya dinga mata nasiha mai shiga jiki, sosai jikinta yayi sanyi saboda kalaman da yayi amfani dasu masu sanyi ta tsigar ban hakuri, da rarrashi sosai taji zuciyarta tayi sanyi tabbas ita din mai mallakawa mukarama diyar cikinta ce koda bata auresa ba. muryarta a sanyaye tace "kayi hakuri nima bansa dalilin kukan nawa ba, Allah ya tayata riko yasa ta zamemata sanyi idaniya, ta zamo alkhari arayuwarsu, ta zamo silar samun nasu na kansu "ameen ameen haka nake son ji, kinyi addua mai kyau Allah ya amsa adduarki . tace "ameen " "kinyi addua amman baki yiwa kanki adduar sake sunbulomin wasu kyawawan baby's din cikin kankanin lokaci ba, suka sa dariya "rufa min asiri ,ce maka akayi haihuwar sauki gareta? "in dai irintaki ce tana da sauki.. kamar kiftawa da bisimilla.. rana suna tun da sanyi safiya aka rad'awa baby sunanta da mahaifinta yayi mata huduba dashi wato aysha ,wanda take mukarama tashiga sheidawa mutane lakanin da take son a dinga kiranta dashi wato muwaddat. gida ya cika makil da dangin hajara da abonkan arziki ,da kawayen mukarama, dan dai su mukarama basu da wasu dangi ,kusan duk danginsu sun riga iyayensu rasuwa , akwati uku mukarama tayi na kayan bby banda wanda ishaq yayi, domin har hall din da akayi suna ishaq ne yakama yayi 'barin kudi sosai kmr shi akayiwa haihuwa ,anyi rabo kamar hauka , manya jakunkuna ne masu d'auke da hoton bby da sunanta rubuce, manya towel kala daban daban da takalmin wanka, duk wanda ka gani a gurin sunan zaka gansa rike da jakarsa . bayan suna da kwana biyu mukarama ta tattara inata inata ta koma gidanta, amman kullun garin Allah ya waye, bata kira hajara ba, ta kirata sau goma domin ta tambayar lafiyar muwaddat ,wani lokacin idan muwaddat tana kuka kafin mukarama ta kira ita zata rigata kira tasanya mata kukanta aiko haka haushi zai kama mukarama, tace "aunty kin iya wulakaci ,amman ki cigaba lokaci dai " hajara ta kwashe da dry"lokaci dai ,to idan kinyi zuciya ki zo yanzu ki d'auke nasan ranki ya 'Baci ,"ki kwantar da hankalinki lokaci kawai nake jira. "ai kuwa nima dana huta haka dai suka yita gudanar da rayuwarsu gwanin ban sha'awa.. akwana a tashi babu wuya agurun Allah har muwaddat ta cika shekara biyu a duniya, ranar alhj mahmud yace "bata k'ara kwana biyu a gidan tunda daman an yayeta ,washegari alhj mahmud ya kira mukarama yace" tazo ta d'auki diyarta, babu bata lokaci ta biyo jirgi kwananta daya ta d'auketa sai burnin iko. d'aki guda aka ware domin muwaddat Wanda ke d'auke da kayan sawarta da kayan wasanta iri iri ,kafin kace mai tuni gidan ya d'auki fariciki da murna, muwaddat bata da damuwa bare kiyuwa duk inda mukarama tayi tana biye daita tana kiran ummi abun ko yayiwa mukarama dadi sosai . a washegarin ranar da aka wo muwaddat tasoma cin karo da tashin hankali a karancin shekarunta, domin kuwa tana bacci motsin ishaq da mukarama ne ya tasheta ,suna tsaka da ihunsu na jin dadi da suka saba da nishi, har sukayi sex suka gama akan idanun muwaddat suna rungume da juna suka yi bacci. shirun da d'akin yayi shi ya bata damar yin bacci.. kullun dare hakan ce take kasance ,ko tayi bacci sai tashi, sai dai bata kuka kasanceearta ba mai fitina bace, a wannan rayuwar ta cika shekara biyu da rabi a gidan . duk inda ummi zata tare take zuwa da muwaddat hatta gurin aiki bata yarda ta d'auki mai aiki ba acewarta lokaci bai yi ba tukunnan sai ta isa shiga makarata . wata rana mukarama na zaune a office dinta tana tsaka da aiki ,yayinda muwaddat ke kwance acikin wani d'an k'aramin gadon na yara tana bacci, taji kamar an tsinkareta aciki, tayi shiru can sai taji kamar cikinta ne ke motsi,sake jin motsin yasa tayi zabura ta mike tsaye jikinta har rawa yake ta nufi d'akin scanning ,daya daga cikin ma'aikatan asibintin tasa tayi mata scan ,aiko take ta tabbatar mata d'a ne acikinta kuma yana cikin koshin lfy . "alhamdullahi kawai take furtawa tana kuka domin tasan adduar ce allah ya amsa, batare da 'bata lokaci ba, ta kira ishaq ta sanar masa halin da'ake ciki, cikin minti goma sai gashi ya bayyana agabanta, suka rungume junansu suna kuka suna murna, hannuwansa duka ya d'aura saman ciki yaji ko da gaske ne, har lokacin cikin bai daina motsi ba, yayi kasa ya kara kunnensa "my baby ,here is your dad, ina sonka baby nah, Allah yasa ina da rabon zanga abinda ke cikin ki mukarama . "allah ka tsare min cikin nan kada wani abu ya sake samunsa, idan na rasa shi bansa yadda zanyi ba , ya Allah karkasa wani abu ya samesa haka yayita addua yana sambatu,kokarin durkusawa tayi itama kamar yadda yake, yayi saurin tarota jikinsa yana girgiza mata kai "ka daina kuka plz addua kawai shine mafuta, yadda take goge masa hawayen fuskarsa haka shima yasa harshensa yana lasar hawayen dake fitowa daga kwarnin idanunta suna ciki haka kamar ance su kalli inda muwaddat ke kwance suka ganta zaune tana kallonsu, ahankali suka mike suka k'arasa gurinta suna rigerigen d'aukarta mukarama na cewa "kin tashi baby? ta d'aga mata kai kawai dan bata magana sai gwarancinsu na yara, shi kuwa ishaq d'aukar yayi ya rungumeta had'e da d'aukar jakar mukarama "oya mu tafi gida aiki kuma ya kare d'an banason wani abu yasamu baby nah.. .. banda alhj mahmud da hjyr ishaq babu wanda suka fad'awa cewar cikin mukarama ya tashi, wata irin sabuwar kulawa yake bata, yana sake riritata kmr kwai ya hanata aikin komai tare da sakawa a samo musu mai aiki ,batare da bata lokaci ba aka samo musu babbar mace mai suna mairo wacce zata zo tunda sanyi safiya , tayi aiki idan dare yayi ta kama gabanta. akwana tashi babu wuya agurin Allah ,har Allah yasa cikin mukarama ya kai wata takwas, tun suna jin tsoro kar cikin ya sake kwantawa, har suka fidda rai suka sakankance da rabonsu ne ciki, sannan alokacin ishaq yayi nadamar abinda yayiwa yan'uwansa akan ciki, saboda babu mahalukin daya isa ya kashe ko ya raya sai Allah. sai a wannan lokacin mutane suka lura da cikin jikin mukarama ya tashi ,wasu daga cikin dangin ishaq basuyi fushi akan furucinsa ba sukayi tattaki domin tayasa murna ya ko ji dadin hakan har ya rokesu yafiya, sannsn yayi marking dinsu amatsayin masoyansa na gaskiya, yayinda mafi yawa acikinsu suka ki zuwa.... cikinta na shiga wata tara yayi wani irin girma na ban mamaki, tashi da kyar, zama da kyar, tayi scanning yafi sau goma ko 'yan biyu ne aciki amman daya ake gani, sai dai yaron tun agurin scanning tasan kato zata haifa. bata haihuwa a wata tara da kwana tara da'akasani ba, sai data shanye wata goma cif sannan mukarama ta haifo salelen danta kin kowa wanda ya rasa, bayan uwar wuyar data sha kmr bazatayi rai ba, domin har ta haifi yaron bata cikin haiyacinta,yaron kyakyawan fari tassss tamkar balarabe, bashi da bambaci da mahaifiyarsa, sai abinda baza'a rasa ba daya d'auko na mahaifinsa. tun tana nakuda ishaq yake sadaka har sanda ta haihuwa bai daina ba, haka muwaddat tunda aka haifi yaron ta d'aura idanunta akanshi taji duk duniya babu halitar da take so kamar shi ,taki yarda kowa yazo gurinsa duk wanda zai d'aukesa sai ta saka kuka "kar a d'aukar mata babybta, rana suna yaro yaci sunan mahaifin ishaq muhammed auwal.. suke kiransa da bunayya. ************ muwaddat na da shekara biyar a duniya har lokacin daita suke kwana a d'aki da auwal da yake da shekara biyu, shi yana gadon jarirai yana baccinsa, ita kuma tana kan gado , zuwa lokacin tasoma wayo da abinda su ummi suke aikatawa a duk daren duniya ,da yadda ummi ke sucking din abi, da yadda zatayi masa gaho har zuwa sanda zasu yi having sex duk tana gani, haka ummi zata dinga nishi uhmmmmmm uhmmmm tana k'ara d'agowa abi kasanta, haka zatayita numfashi kamar mai shirin haihuwa duk wannan abinda suke Allah bai ta'ba nuna masu cewar akan idanun muwaddat sukeyi komai ba, har suyi su gama idan ihunsu yayi yawa ne ma take toshe kunnuwanta. sai datayi shekara bakwai sannan ta koma d'akinta da kwanciya ganin haka shima auwal ya tubure yace bazai kwana agurinsu ba, sai tare daita zai kwanta, dan haka ummi ta barsu, tunda ummi ta haifi auwal bata sake samun ciki ba haka zalika hajara itama shiru babu haihuwa sai akram dake gurin shekara takwas a duniya.. ********** auwal da muwaddat sun taso cikin kulawa da soyayyar iyayensu babu irin gatan da abi baya musu ,komai ya gani muwaddat da bunayya, duk abinda suke so zai siyo musu ,kama daga yawo zuwa kayan wasa duk suna dashi, sai dai dukkaninsu miskilaye, abi na ganin miskilanci muwaddat , amman sai yaga har na muhammed auwal ya doketa, dan da fari sun d'auka kurma ne baya magana ,saboda silent dinsa yayi yawa,sai daga baya daya isa shiga makarantar suka fahimci miskili ne kawai ke damunsa . shekarasa uku alokacin, amman idan ka gansa zaka d'auka shekarunsu daya da muwaddat saboda yanayin girman jikin da Allah yayi masa, hatta joystick dinsa wata irin murd'ad'iya ce as age of 3yers , idan muwaddat ta d'auke ajikinta da sunan wasa yanzu joystic dinsa zata mike tayi wani irin girma, an sha fama dashi lokakacin da aka kai shi makaranta da muwaddat take zuwa, dan kuka ya saka ba zai zauna ajin da aka kai sa ba, sai dai class din su muwaddat, ko an kai shi ajinsa sai ya dawo ,haka malamai suka gaya ummi tace kawai abarsu a class daya .. haka suka taso cikin shakuwa da son juna,idan daya bai da lafiya dole daya ma yayi, idan ka gansu zaka d'auka tagwaye ne saboda kamar da suke da juna ,gashi komai nasu iri daya hatta yanayin murmushi banbacinsu, ita muwaddat chocolate colour ce shi kuma fari ne tasss tamkar jinsin larabawa .. abu kamar wasa duk daren duniya muwaddat da bunayya basa bacci suna makale da juna cikin bargo, muwaddat na wasa da joystic dinsa kmr dai yadda taga ummi nayiwa abi, wani lokacin har sha take ,shi kuma sai yayi shiru ,yayita kallonta ,alokaci idan ummi nayiwa bunayya wanka idanun muwaddat na kansa tana kallon joystic dinsa wani so take masa komai tace kaninta bunayya tare suke komai .. cikin haka kanin abi da suke uwa daya uba daya ya kawo musu ziyara daga london ,yaci karo da wannan tashin hankali da su muwaddat suke, sake ware idanunsa yayi lokacin dan tabbatarwa kansa abinda ya gani, mafarki ne ko gaske? cigaba da kallonsu yayi cike da matsanancin mamakin ,suna romancing junansu muwaddat na wasa da joystick dinsa shi kuma yana wasa da gabanta ,alokacin dai shi yasan basa jin komai, asalima basu san me hakan yake nufi ba,zuciyarsa tayita masa sake sake hade jero masa tambayoyi, shi yasan duk yadda akayi sunga wani yayi ne agabansu shiyasa sukayi, bai d'aura laifin akan kowa ba sai akan yayansa, yayi tunanin idan ya bar su tare ,haka zasu yita har girmansu , dan haka ya yanke shawarar idan zai koma zai wuce da bunayya ya hadashi da yaransa tunda duk maza garesa .. da lokacin komawarsa yayi umar yasamu dan'uwansa akan yana son ya tafi da muhammad auwal domin yayi karatu acan london, abi bai so rabuwa da d'ansa ba, sai da umar yayita rarrashi sannan ya yarda, yasan is not easy rabuwa d'a ,d'an ma kuma tsoka daya a miya amman wannan tafiyar da zai yi dashi shine kwanciyar hankalinsu. ummi ma tashiga damuwa sosai ,alokacin tausayin hajara ne ya kamata a she haka taji lokacin da taje ta d'auko muwaddat, tunda aka tafi dashi muwaddat tashiga damuwa har da ciwo tayi.. Muhammad auwal dai ya bar kasar Nigeria, sai dai ya yafi kwal'kwaluwarsa d'auke da abubuwa masu wuyar mantawa. bayan tafiyarsa muwaddat ta dawo wani iri sam bata da walwala, komai cikin sanyin jiki take , ummi tasa aka samo mata malamin addini wanda zai dinga zuwa har gida yana koyar daita, school daman ita ke kaita, wata irin kulawa da tsaro ummi ke bawa muwaddat ,wanda ta kasance duk sanda zata shiga cikin mutane zaka ga tana d'ari d'ari dasu had'e da jin tsoro , hatta malamin dake zuwa koyar daita baya zuwa sai tana gida ,sannan tana zaune a parlour'n tana kallonsu ake karatun ,bata zuwa koina kullun daga school sai office din ummi sai gida a haka taso... Muhammad auwal kuwa suna zuwa kasar london uncle dinsa ya sanyashi makarantar da yaransa ke zuwa . muwaddat ta girma da matsanacinyar sha'awa da soyayyar bunayya acikin zuciyarta , komai take yana cikin ranta, wannan sha'awar ta haifar mata da matsanancin ciwon mara mai tsanani , alokacin da zata soma jini sai abun ya sake karuwa , ummi da kanta ta d'aurata akan magani, muwaddat na da kokari sosai ta fanni karatun addini da boko amman batason karatu sam, duk lokacin da zata makaranta ranta idan yayi dubu sai ya baci, haka idan malamin addini yazo ta dinga shiririta kenan kafin ta fito, bata ta'ba zuwa na biyar ba sai sama da haka a makaratar boko , ba wai dan bata da kokari ba, sai dan tsanar karatun datayi yasa bata maida hankali,haka ummi zata tayi mata fad'a ,har tambayarta ummi tayi, ta fad'a mata abinda take son ta siya mata dan dai ta dinga karatu sosai , bud'ar bakinta muwaddat tace "waya "ummi tace "mutumin da bai da waya bai maida hankalinsa akan karatu ba ina ga an siya masa waya? "idan dai kina son waya kiyi k'okari wannan karon kizo koda na biyar ne ni kuma nayi alkwarin zan siya miki , aiko muwaddat ta tashi tana tsalle had'e da jin dadi dan kusan rabin yan ajinsu suna da waya ita kadaice bata da.. bayan sun koma makaranta take gayawa wata k'awarta kausar abinda umminta ce dan haka zata maida hankali sosai wannan karon ,muwaddat ta takura kanta da karatu babu dare, babu rana , lokacin da sukayi jarabawa sai gashi tazo na uku ranar har celebrating akayi agidan , ummi ko ta cika mata alkwarinta ta d'auke suka nufi ikija ,cikin manya slot ta siyo mata hadadiyar wayarta sumsumc.. Muhammed auwal bai dawo kasar haihuwarsa ba, sai bayan sheheka goma sha shida alokacin yana shekara sha takwas cif a duniya, lokacin daya zo hutunsa na farko alokacin muwaddat ta girma ta zama budurwa komai yaji ajikinta, tana daf da kare secondary school shima haka kallonta ya dinga yi abubuwan da suka faru abaya atsakaninsu na dawo masa,duk inda tayi idanunsa na kanta boobs dinta sun girma fiyye da yadda yake ganinsu acikin kayanta idan suna video call, haka Hip's, a lokacin duk yadda yaso wani abu yashiga tsakaninsu taki, sai ma tsokanarsa da take da kaninta, shi kuma abinda yafi bakanta masa rai kenan,ya tsani tana kiransa da haka. yagama hutunsa ya koma batare da wani abu yashiga tsakaninsu ba ,sai dai ya hango saman dukiyar fulaninta daga saman rigarta sai kuwa bombom dinta daga cikin kaya..... a wannan shekarun na Muhammad auwal babu kalar nonowan da idanunsa basu gani ba saboda ,farinjini da Allah yayi masa ,yammata da kansu suke kawo masa kansu ,amman cikinsu babu wacce yake jinta tamkar muwaddat a zuciyarsa, lungu da sako duk inda yasan zai samu video na bf da hotona duk yasani haka zai tara abokai suyita kallon tsiranci hotonan turawa, duk macen da tace tana son shi kuwa, muddin kina son shi da dukkanin rayuwarki da zuciyarki, dolenki ki d'auki hoton tsirancinki ki tura masa wani lokacin idan yana kallo har imagine yake as shi da muwaddat ne a dalilin wannan tunanin har zai kawo batare da yasan hakan ta faru dashi ba . duk da wannan iskanci nashi bai ta'ba saduwa da diyar kowa ba saboda yana da buri acikin ransa ko romacing din mace bai yi saboda kyakyami garesa, sai dai a bud'e masa nonowa a zahiri ya kalla ,idan mace tayo tsirara agabansa tana fama da manya nonuwa da hips da komai sai dai ta tsaya iya haka ya kalli tsirancinta, amman batu na sex bazai yi ba , har kuka suke masa suna rokonsa yayi having sex dasu kasancewar Allah yayi masa wata irin kira mai zaburarwa ,duk macen data kallesa sai taji sha'awarsa ta tsarga mata ,wani irin hallita garesa mai shiga rai da tsayawa a zuciyata ,gashi dai yana fama da tarin sha'awa domin wani lokacin idan sha'awa ta sakoshi gaba kwana yake da ciwon ciki sai ya kai ga shan tablet ko yayi allura, sannan yake samun natsuwa. haka abokansa zasu yita masa korafi "me yasa yana da damar da zai biyawa kansa bukata amman zai ki? "ina ma sune suka samu wannan damar ai babu abinda zai hanasu damawa, haka zaiyita jinsu amman shi sam baya jin zai iya cin daya daga cikin yammatan dake kawo masa hari.. itama bangaren muwaddat haka take fama da muguwar sha'awar idan abun ya tasar mata haka zatayi ta nukurkusun ciwon mara. lokacin data kammala secondry school dinta alokacin aure taso ayi mata ,amman iyayenta suka sai mata form din jamb ,tayi kuka tayi bakiciki wannan karatu dan haka data je rubuta jarabawarta taki rubuta abun kirki , aiko lokacin da result ya fito iyakacinta poly , ummi tayi bakinciki mara misaltuwa tayita mata fad'a kmr zata bugeta .. a koda yaushe suna waya da muhammed auwal har ma da chartting tun bata sakewa dashi har tazo idan ma bai kirata ba ita zata kirasa wata irin shakuwa ce atsakaninsu ta dawo mai ban mamaki kowanensu ya girma da burin son mallakar ,mai yanayi da tsari irin na danuwansa..... yadda muhammed auwal ke mugun son muwaddat haka faiza kanwarta da suke uwa daya uba daya take mutuwar son shi sai dai shi ko kallo bata, ishe shi ba, duka guda nawa take ? " alokacin duk shekarunta basu haura shabiyu ba shi dayake dil da manya mata mai zaiyi da kamar yarinya kamar faiza? " mai zata yi masa yaji dadi dan haka ko sau daya bai ta'ba tunanin zai saurareta ba ... duk karshen shekarar duniya bunayya zai kawo musu ziyara, duk kuma saboda muwaddat yake zuwa amman har wannan lokacin bai fito ya bayyana mata komai ba za dai suyi wasa da dariya har ma da kokuwa idan takama ,wanda a haka yake samu ya karewa halitar jikinta kallo son ranshi... .. mmn sudais [12/23, 5:19 PM] +234 808 651 9747: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU AYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ warning!!! don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you read it, is for your own risk ...... WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim page 6 back to the store.... bakin ummi d'auke da sallama tashiga cikin had'ad'en parlour'n gidan inda ta iske hjy hajara na zaune tana faman yiwa muwaddat fad'a kmr zata bugeta , sallamar ummi ce ta katse fad'an da take mata ,atare suka amsa mata sallamar sannan muwaddat ta mike da cikin sanyin jiki ta rungume ummi tana zuba shagwaba tace "ummi nah oyoyo sannu da zuwa ,nayi kewarki ta fad'i hk muryarta a raunane tmkr zatayi kuka duk da tana cikin murnar ganin ummi amman kana ganinta kasan ranta a 'bace yake .. lokaci daya ummi ta fahimci tana tattare da matsananciyar damuwa, amman hakan bai hanata jin wani irin sanyin dadi aranta ba, duk duniya babu halitar da take so kamar muwaddat " rayuwarta ce muwaddat, domin kuwa ta sameta kafin tasamu duk wani farinciki daya danganci jin dadin rayuwa a bangaren ya'ya, zareta tayi ajikinta ta kamo hannayenta a rud'e suka isa kan kujera ta zaunar daita kana ta zauna tana ajiye jakar hannunta ,sannan ta tsura mata ido tana dubanta fuskarta d'auke da tambayoyi.. "ki dai mata fad'a ba tsura mata tsumammun idanunki zakiyi ba, koda yake ai duk kece kika lalatata , in ji cewar hjy hajara " "haba aunty hajara yaya kuke son nayi da yarinyar ? ke da yaya kun sata gaba da damuwa ,nima shine kuke son na damu rayuwarta? "shiyasa bata kaunar zuwa gidan nan nake matsa mata zuwa hutu . "daman wa yake bukatar ganinta, kema kinga damar zuwan nata ne, data zo da karta zo duk daya ne agurina ,matukar dai yarona auwal zai zo garemu meye idan ita bata zo ba? muwaddat na gama jin abinda mahaifiyarta ta fad'a ta rushe da kuka . Ummi ta dubi hjy hajara ranta a matukar 'bace tace "gsky aunty hajara bason irin abinda kuke yiwa yarinyar nan, karatu ne dai dole tayi domin inganta rayuwarta, amman duk wani takura bashi bane maslaha ba , karku damu tunda abun yazo da Kora da hali yanzu zamu yi tafiyarmu,mu bar muku gidanku " ko ba shikenan ba ? "ku fi jirgin sama tafiya ,Idan ma kun tashi tafiyar kar ku tsaya a kasar nan, ku bar kasar gabadaya nan zan San ranku ya 'baci ,ta juya fuuuuu ta shige cikinn d'akinta . shiru ya biyo bayan tafiyar hjy hajara ,kafin daga baya ummi ta kamo hannunta duka cikin nata ta kira sunanta ahankali "muwaddat meke damunki akan rashin son karatu haka? Kukanta ya tsananta har da shesheka ,ta goge hawaye wasu na sake gangarowa ,ummi ta runtse idanunta saboda jin zafin yadda take zubda hawaye akan abinda itace zata ci gajiyarsa a karshe, ganin kukan nata yaki tsayawa domin hawayenta har saman hannunta take jin digarsa, ta bud'e idanunta da kyar tana sake dubanta "kinga ba kuka na tmbyeki ba"me yasa baki son zurfafa karatunki simple as that ? Muryata cike da kuka tace "babu komai ,ni dai haka kawai na tsinci kaina da rashin son karatu, ta k'arasa mgnr tana sake rushewa da wani matsanancin kuka. "ki tsani karatu muwaddat ? ummi ta maimaita tana kallonta, muwaddat ta d'aga mata kai ala'mun" eh"tana sake rushewa da kuka tamkar wacce aka aikowa sakon mutuwa. "is okay banason jin kukaki yana ta'ba min zuciya .. "to me zakiyi idan bakiyi karatu ba arayuwarki ? " ko kuma aure kike so...? wata irin matsananciyar kunya ce ta kamata , tabbas idan da zasu barta ,ita kan aure take so akan karatu,tafi son tayi aure fiyye da komai ,but ba zata iya furtawa umminta haka ba,bazata iya kallonta idanunta ta fad'a mata abinda ke cin ranta ba ,idan ma ta furta ,wa zata aura a halin yanxu? ita da bata kula kowa. "kinyi shiru kina tunani idan aure kike so ki bud'e baki ki sanarwa umminki ? "bazan hanaki yin aure ba, amman kisani auren wannan zamanin yana bukatar jigo acikinsa ,domin baki san wand zaki aura ba tukunna , kiyi k'ok'ari ki zurfafa karatunki so that idan ma auren zakiyi sai kiyi, kina cikin karatunki"amman zance aure yanzu bai ma taso ba ,Sam Sam idan ma shine aranki gara tun wuri ki cire kiyi abinda zai fisheki da rayuwarki .. Ganin muwaddat tayi shiru taki cewa komai har na wasu yan mintuna ,yasa ummi ta sake jeho mata tambaya "ko akwai wanda kike so ne bamu sani ba ? muwaddat tayi saurin girgiza mata kai alamar "a,a" "to meyasa ba zaki saki ranki kiyi karatunki ba? " duba yan mate dinki , kowace yanzu tana mataki na uku a jami'a amman ke sam kin kasa maida hankalinki, idan fa ba zaki maida hankalinki akan karatunki ba ,wallahi zan zare hannuna acikin lamarinki" " haba yarinya sai fama ake dake akan abu daya meye illar yin karatu baya ga martabarki da zai k'ara a idanun duniya ,karatu shine komai duk da shima auren yana da muhallinsa, but at least ki tsaya kiyi facing din karatunki "kalleni a yanxu babu abinda yasa na taka matsayin da nake sai karatu, fad'a ummi tashiga yi mata sosai ta inda take shiga ba nan take fita ba . muwaddat ta zube kasa bisa gwiwowinta tana kuka "ummi kiyi hkr na tuba ,dan Allah karki cire hannunki acikin lamarina, ni dai karatun ne kawai banaso, amman daga yau nayi miki alkwarin zanyi, zan tursasa zuciyata, zan saka lamarin karatu acikin raina.. "idan ki kayi min haka zan ji dadi sosai , domin shine burin ahlinki ,gabad'ayanmu burinmu bai wuce muga mubaki tallafi na ingantaccen ilimi arayuwarki ba , dan baki da wani gata da yanci daya wuce karatu. "matukar kina son mu shirya dake ki saki ranki ki saka soyayyar karatu aranki " "Inshaallahu ummi zanyi karatu har sai kince ya isa tunda shine farincikinki ,"ok tashi kije ki soma had'a kayanki nan da awa zamu bi jirgin karfe biyu , jikinta a matukar sanyaye ta miki tasoma daga zararan kyawawan yatsun kafafunta ta nufi hanyar d'akinta har tashige idanun ummi na kanta tana sake nazarinta, domin gano takamaiman abinda take so ,da yasa ta tsani karatu, bayan ga million's of people out there suna neman wanda zai tallafawa rayuwarsu su yi . Mikewa ummi tayi ta shiga d'akin hjy hajara tana zolayarta "gsky aunty banason irin abinda kikewa yarinyata, ina dalili wannan takura ?" Sai naji saukar ko duka tukunna zan San baki son abinda ake mata,kuma ni ina ruwana aciki? "daman yayanki nake tayawa yakin shiyasa kikaji bakina "Allah ko? "to kijira wannan karon ba duka zanyi miki ba aure zan yiwa yayana in ga kashe bakin tsiwa. "drya ce ta subucewa hjy hajara aiko tashiga yi "daman nasan duk matakin bai wuce haka ba ,Amman dai kin sani ba tun yau ba ,ni hajara bani tsoron kishiya, a da can ma ban ji tsoron zuwanta ba ,sai yanzu Dana San kota zo babu abinda zata tarar na gama tsotse komai ... suka sa driya gabadayansu suna tafawa ,kana suka shiga halin nasu da suka saba na shakiyanci a junansu ,sannan daga baya suka shiga wata hirar.. Ita kuwa muwaddat tana shiga d'akinta,a madadin ta had'a kayanta kmr yadda ummi ta bata umarni ,sai ta fad'a kan makeken gadon ta kwanta ruf da ciki ta rarumo pillow ta manne ajikirjita tana jin wani iri agabadaya ilahirin jikinta, hannunta daya tasa ta lalu'bo wayarta dake yashe agefe ,ta kunna tana duba screen din wayar miss Call ,tagani rututu akalla zasu kai guda ashirin, kuma duk na M.A ne. jikinta na rawa tashiga nema layinsa kira daya biyu ya ya d'auka yana sauke naunayen ajiyar zuciya had'e da buso mata iskar bakinsa Wanda hakan yasa gabadaya Gabobin jikinta mutuwa ,sai dai lokaci daya hankalinta yayi mugu mugun tashi saboda shirun da yayi yaki magana,tsawon minti goma suna haka batare da suncewa juna qala ba ,illa numfashinsa dayake aikin buso mata ,suna kashe mata sansar jiki ,take kirjinta yashiga wani irin mahaukacin bugu da karfi gaske ,sakamakon rashin jin sautin muryarsa. Jarumta ta Nemo ta sanyawa jikinta ,kana ta bud'e bakinta da kyar ta kira sunansa "auwal dan Allah kayi min magana shirunka na d'aga min hankali " "a wani dalili hakan zai d'aga miki hankali, tun dani ba kowa bane agurinki , at least mis call nawa nayi miki?" haba muwaddat kinsa yadda zuciyata taji alokacin kuwa? "kayi hakuri ba laifina bane ni kaina bana cikin natsuwata, duk abinda nayi ina yinsa ne kawai amman hankalina na gurinka ... takarasa mgnr cikin rawar muryar kmr zatayi kuka, kana ta kashe kiran . ta rike wayar a hannunta tana jujjuyawa tana tunanin wasu abubuwa dake faruwa atsakaninta da M. A.... hawaye ne yashiga gangarowa daga cikin kwarnin idanunta "tana mugun son M. A amman tasan soyayyar tasu babu abinda zai haifar ,M. A kaninta,sannan ba lallai iyayensu su yarda da hakan ba ,Dan haka tayiwa kanta alkwarin zata tsaya tayi karatunta tunda shine burin iyayenta ,ko bama haka ba ita kanta zata fi son farincikinsu Akan nata .. ******** Tun daga wannan lokacin muwaddat ta maida hanakalinta akan karatunta hatta M. A ta tattarashi ta ajiye a gefe daya, ko ta hau online bata shiga contact dinsa sai dai tayi abinda zatayi ta sauka,idan ma ya turo mata sako bata wani bashi full time dinta ,sama sama zata bashi amsa , shima a bangarensa yana tsane da sabon salon datazo masa dashi Amman ya shareta saboda shima yana jina zafinta a game da katse masa wayar da tayi ,amman ganin idan suka ta tafi a haka shi zai fi cutuwa ,yasa yau yayi shawarar kawo karshen abun ,ya turo mata da sakon vioce note ta WhatsApp . " ni wallahi muwaddat ina da matsala guda daya da ke, ni bansan abinda ya faru ba kika juya min baya ," ni me nayi miki ne ? "da bakya son kiyi magana dani ni ban San laifin da nayi miki ba, idan wani abu, ni keda alhakin yin fushi dake ,"ni dalibinki ne muwaddat ni yayanki ne ,ni Dan gatanki ne Dan Allah muwaddat, Dan Allah ki daina min haka kinji ki bari mu cigaba da abubuwanmu kmr yadda mu keyi tun farko ,rabon da muyi hira dake mai dadi tun randa da zaki bar ilori ,yanzu sam na lura baki da lokacina . ,haba muwaddat kema ki duba kigani mana ,ina wata kasa ina bukatar kulawrlarki... ya k'arasa yana Jan mgnr da sakin numfashi sannan ya tura mata ... Cikin minti biyu ta turo masa da sako "kace dai muryarta kake son ji ? "Alamar dry ya turo mata sannan ya rubuto mata "eh. "okay ina zuwa .. Cikin sauri ya rubuta mata "no ki tsaya plz ni so nake muyi hira .... "Okay Dan kanina gani kusa anything for, wace irin hira kake son muyi ?yana jin ta fad'i hk ya ki rata ta d'auka had'e da yin sallama, batare daya amsa ba yace "Idan fa kina cewa Dan kaninan naki za'a d'auka fa wani yaro ne qarami ,gwada dai ki dinga cewa yayanki kawai kiyi shiru kinga mutane bazasu d'auka Dan kani bane ,Dan ni ba Dan kankani bane wallahi.. "gsky kwanakin kin wahalar da zuciyata, ki dan mun magana naji muryarki ko zata dawo min da natsuwata , "ko ka yarda ko karka yarda ni auntynka ce shekara uku zuwa hud'u ba wasa ba, murmushi yayi yace "matukar na kiraki da wannan kalmar na gama rusa cikar burina dana girma dashi muwaddat, sannan karki manta an samu cikina tun kafin asan za'a dasa naki kwan, Allah kad'ai yasan abinda yake nufi, daya kwantar da cikina ya tada rayuwarki, "dana rigaki zuwa duniya kinsa shekaru nawa zan baki? ta yatsina fuska tana ta'be baki kmr tana gabansa tace "kana son girma dayawa auwal, ina jin da'ace ka girmeni da bansan yadda zakayi ba "no no wannan ba zance son girma bane, koda kin girmeni, zan iya girmanki ta wani bangaren ,saboda ni namiji ne dan haka ki daina tunanin ni kaninki har abada ni yayanki ne saboda na girmeki aciki... "ni kuma ba girmeka a haihuwa ba tana gama fadar hk ta katse kiran daman shirin kwanciya take, ta kwanta lamo tana jin jikinta wani irin mika tashigayi wani irin mahaukacin feelings na taso mata ahankali dai har bacci barawo yayi nasarar d'aukata .. ****** sannu ahankali M.A yake janta ajiki batare da ta fahimci komai attare dashi ba, wata irin sabuwar shakuwa ce mai karfi ta sake shiga tsakananin muwaddat da bunayya, komai ya gadamar fad'a mata fad'a yake batare da jin kunya ko shakkanta ba, sai ma itace take nannakewa a wasu lokunta, saboda matsayin dayake dashi agurin uwa uba ita magana ba damunta tayi ba. kamar kowani daren duniya daya saba kiranta a waya hakan ce takasance yanzu, batare da 'bata lokaci ba ,ta d'auka a natse muryarta ta doki dodon kunneshi " assalamu alaikum kanina ? "ya gida da karatu 'd'an kanina ? "D'an mara kunyar kanina ta k'arasa mgnr tana hamma "na soma gyangyad'i bacci nakeji fa"ta k'arasa maganar tana kashe masa murya take joystick dinsa ta Mike kyam, yayi saurin d'aura hannunsa d'aya akan joystick dinsa ya dafeta,yana murmushi kmr tana gabansa ,muryarsa a tsarke ta fito yace "maganarki ta saukar min da kasala gabadaya , sai naji kmr ina ma najini acikin jikinki ina romancing dinki plz muwaddat karki hanani jikinki duk ranar Dana dawo ,idan ma da hali ki barni nayi yadda nake so dake " "Kamar ya kenan na barka kayi yadda kake so dani karka manta ni yayarkace "and so what idan ke yayata ce, wallahi matukar zaki barni zan tabbatar miki da zan ci.....ya katse maganar yana furzar da numfashi. Jin yayi shiru yasa ta janyota numfashi ta fesar kana tayi kasa sosai da muryarta tace "bunayya ka daina tunanin zaka iya cina ,ai ka fahimta ? "'kwa'kwaluwarka ta daina hasko maka zaka iya cina ,ko kuma zan bari ka cini ,saboda bazan ta'ba cuwuwa ba agurinka, tana magana dariya ta su'buce mata " bazaka ta'ba kusantata ba, nmj da zai iya kusantata daban yake bawai rainaka nayi ba , ta cigaba mgn "gaskiya Wanda zai iya sarrafani bakaramin gwarzo bane .. murmushi ya dinga yi yana jin ina ma suna tare daya nuna mata shi din ya zarta gwarzo "muwaddat .... "na'am " " ina son nono kinji baby nah ya k'arasa mgnr muryarsa tmkr mai shirin yin kuka ..tayi shiru ta kasa ce masa komai, ya sake kiran sunanta " Ayshatul muwaddat .......... Wani irin zrrrrrrrr taji ajikinta saboda yadda ya kira sunanta gbdy tsigar jikinta ya Mike, da kyar tace "na'am bunayya .. "ina son nono pls........................... "Na had'aki da girman Allah karkice a'a ni dai kawai ki turo min su ina son gansu ,nayi matukar kewarsu, wallahi idan bangansu ba komai zai iya faruwa dani ,muwaddat ina son brest dinki ,suna mugun rud'ar dani a duk lokacin Dana kallesu, yanzu haka bakiji yadda nakeji ba ,komai nawa ya sauya joystick dina ta mike taki kwanciya nasan ganin brest dinki kawai zai sa ta kwanta kinji muwaddat dina duk wannan mgnr da M.A ke yi hannunsa na dafe da joystick dinsa da ta sake mikewa kmr ana hurata.. muwaddat tayi shiru taki ce masa komai domin lamarinsa nason fin karfinta duk yadda take da tsanani bukata M. Aya zarta fiyye da tunaninta. Mmn sudais ce [12/23, 8:22 PM] +234 810 118 7859: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU AYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ warning!!! don't read this novel , if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you read it, is for your own risk ...... WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim page 7 .....muwaddat.. ya sake kiran sunanta cikin raunanniyar muryarsa mai kashe sansar jiki ,da aikawa kwal'kwaluwa wani sako na daban. wani irin bugawa gabanta yayi da karfin gaske, lokacin dataji sautin kiran sunanta da yayi , daga bisani kirjinta yashiga dukan uku uku,"muwaddat ina sha'awar mu kasance tare dake, dan na jibanci al'amuranki da komai na rayuwarki, muwaddat tsarinki da komai da jikinki, komai da kika mallaka sun yi min arayuwa, "me zai hana ki bani wata dama domin na kasance tare dake? nan take tashiga kokuwa da numfashinta dake barazanar d'aukewa sannan ahankali tashiga girgiza masa kanta tmkr yana kallonta.. "kinyi shiru , kin barni sai magana nake ni kad'ai, kice min wani abu mana ko zan samu sausauci da natsuwar zuciya? " ,wallahi ina jin wani abu ajikina daya danganci rayuwarki, zuciyata ta soma wani tunani akanki, a wasu lokutan ina jin tamkar ana fixgar raina akan lamarinki, har na kan zauna na dinga tambayar kaina me yasa nake yawon damuwa dake? duk maganar dayake batayi k'ok!arin bud'e bakinta don bashi amsa ba, illa jikinta dake tsuma tana sauraron maganarsa daki daki. "plz muwaddat ki bud'e baki ki min mgn, kema ki fad'a min yadda kike tunanin yadda rayuwarmu zata kasance anan gaba da kuma yadda kike jina aranki , saboda yanayin danake ji akanki yasoma zarta tunanina.. .. .. "auwal........ "na'am baby ... ...... ya amsa muryarsa can kasa tamkar mai cutar asma" "auwal ka daina yi min magana irin haka ,domin kana kashemin sansar jiki, gabadaya sai na rasa abinda ke damuna akanka, yanzu dai mu bar wannan maganar yaushe ne dawowarka zata kasance? naunayen ajiyar zuciya ya sauke da karfi tare da furzar da wani numfashi mai zafi, sannan ya runtse tsumammun idanunsa wanda suka soma canza kala tsabar jarabar dake cikinsu ,ahankali kwal'kwaluwarsa tasoma hasko masa yanayin tsarin jikinta da kyawun halittarta, dirin jikinta da komai nata har zuwa kan madaidatan bombom dinta dake rud'ar dashi a duk sanda ya kallesu . cikin sanyi jiki ya kamo lip's dinsa na kasa yayita tsotsa yana cigaba da murza kan joystick dinsa ,tsawon minti goma yana haka sannan ya cire hannunsa ya d'aura saman goshinsa yana Shafa sumar kanshi zuwa keyarsa kana ahankali ya bud'e bakinsa da kyar yace "karki canza min akalar maganata ...... "abinda kika sani ne auwal bayason haka, nasan sarai kinsa inda maganata ta dosa amman kike k'ok'arin canza min ita zuwa wani bangare daban "ni kawai mu dawo maganarmu , dan ni ta fiyye duk wata magana ,da zance wani dawowata, "ki amsa min tambayar danayi miki. "magana kace nayi auwal kuma nayi, tmbyr dawowarka is part of magana so me kake son nace maka ? " kice komai daya danggancemu ,ki fad'a min yadda kike jina a zuciyarki . "yadda nake jinka fa kace ? yace "uhmmmmmm ya bata amsa da hakan had'e da janyo pillow ya rungume akirjinsa yana jin kmr ita ya rungume "ta runtse idanunta sannan tasoma mgn cikin sanyayyiyar muryarta wace take saurin kashe masa jiki a duk sanda tayita numafashisa yashiga sauke da sauri sauri yana sake rungume pillow kmr wanda za'a fixgewa. "bana jin komai a game dakai daya wuce soyayya irinta 'yan'uwantaka da kuma shakuwar da zumunci mai karfi ba that's all... "bakya jin komai akaina daya wuce soyayya ta yan'uwantaka yayi saurin katseta ta hanyar fad'ar haka sannan yacigaba "amman kike iya mallaka min komai daya zamto soyayyyar zuciya da zuciya ce kad'ai kan iya haifar da hakan "kina sona muwaddat so kuma mai girma, amma tunda kin ajiye soyayyar tawa a muhalin yan'uwantaka shikenan sai da safe ... ..... "no ka.. .. tun kafin tayi yunkurin cewa wani abu, kit taji ya kashe wayar ,tayi zaune Shiru agurin tana duban screen din wayar dake rike a hannunta. "wayyohhly Allah yayi fushi, "to me yasa zai yi fushi dani? tayiwa kanta tmbyr. jikinta yayi mugu mugun sanyi, hankalinta ya tashi matuka, jikinta ya sauya ta kasa jurewa maganganun daya fad'a mata "tabbas dan so tasan tana son shi fiyye da komai dake cikin duniyar nan "but wannan shine babban abun kunya dazata aikata arayuwarta . abun kunya ne gareta ace ta bayyanawa kaninta wannan soyayyar......" amman ai kina iya bayyana masa wasu shashi na jikinki ,wannan shine babban abun kunyar gareki ? zuciyarta ta jeho mata wannan tambayar. zamewa tayi ta kwanta lamo akan katifar ta tana fidda numfashi sama sama yayinda idanunta suka cicciko da hawaye"auwal ina sonka fiyye da komai arayuwata , ina cikin shaukin kaunarka ,wanda bansan ranar da zan daina maka wannan soyayyar ba ,amman basan yadda zan bayyana maka ba..... hawaye ne yashiga gangarowa shar shar bisa kuncinta tana gogewa wasu na sake biyo kuncinta ,muryarta cike da matsanancin kuka "ina matukar sonka auwal ina sonka ... ta furta hkn a fili zuciyarta na dokawa . ranar sam kasa runtsawa tayi duk inda ta juya fuskarsa take gani da komai nashi yana mata gizo, bata ta'ba tunanin soyayyarsa zata mata kamu mai tsananin irin haka ba . yadda bata samu runtsewa ba, haka shima bangarensa kusan raba dare yayi yana faman aiki a kan system da watsawa jikinsa ruwa domin kwantar da sha'awar dake cinsa, kafin ahankali bacci ya fara fixgarsa ya tattara komai ya ajiye ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya. pillow ya janyo kmr koda yaushe idan zai yi bacci ya rungume ajikinsa har sanda bacci ya d'aukesa tattare da tunanin muwaddat . washegari bata tashi da wuri ba saboda rashin ishashen baccin da bata yi ba, k'arar knowking din da akewa kofar d'akinta ne ya farkar daita, "muwaddat muwaddat!! ......." cikin muyar bacci ta amsa "na'am ummi had'e da yin mika.. "ki tashi mana lokacin tafiya makarata na wucewa fa "o...kay ummi na tashi ai, ummi na jin haka ta juya ta koma bangarenta . tashi tayi da kyar ta zauna ta ziro kafafunta kasa tana mai dafe ha'barta dan har lokacin bacci bai fita cikin idanunta ba ,ta mike cikin sanyi jiki ta nufi bayi ta tasoma yin brush sannan ta had'a ruwan wanka. byn tayi wanka ta fito,ta shafa mai, essential fairness softening snd body lotion,sannan ta shirya cikin wata had'add'iyar riga da siket sai doguwar abaya har kasa data d'aura a saman kayan ta yane kanta da mayafin abayar . ta k'arasa gaban mirrow ta kai hannu ta d'auko turare mai shegen karfi ,ta feshe gabad'aya ilahirin jikinta ,ta d'auki jakarta ta rataya ta d'auki wayarta ta kunna ta dawo kan resting chair ta zauna tana duba sakonin cikin wayar ko zata ci karo da sakon M.A amman babu . shiru tayi kmr ta kirasa wani bangare na zuciyarta ta gargadeta da aikata haka , dan haka ta mike jiki a sanyaye ta bar d'akin zuwa parlour'n tana fitowa ta hango ummi da abi zaune a dining har sun fara breakfast saboda rashin k'arasowarta,cike da girmamawa ta isa garesu ta gaishesu daya bayn daya kana taja kujera ta zauna tana yatsina fuska , ummi ta d'ago ta du'beta ta d'anyi murmushi domin tasan abinda ke damunta girgiza kai kawai tayi tasoma saving dinta kmr yadda ta saba, ta turo mata plet din abincin gabanta "maza maza ki cinye lokaci na tafiya, muwaddat ta runtse idanunwata kad'an tana sake yatsina fuska kmr wata k'aramar yarinya "ummi... ta kirata cike da shagwa'ba atare suka d'ago daga ummi har abi suka tsura mata ido domin jin damuwarta " "bana jin cin wannan abincin....... ummi ta dubi abinci wainar masa ce wacce taji naman kaza da alaiyahu idanunta na kanta har lokacin tace "to me zaki ci ki fad'a yanzu nasa mairo tayi miki. tayi kasa da muryarta sannan tace "jollof din spaghetti zan.. ... "kinyi late fa mamana har yaushe za.... "no kira mairo tayi mata kawai inji cewar abi, ba koda yaushe mutun yake jin cin irin wad'an abincin ba most especial alokacin breakfast " batare da bata lokaci ba ummi ta kira mairo ta bata umarni dafa mata abinda ta bukata cikin lokacin kankani mairo ta kammala ta kawo mata. gurin cin abinci ma sai da ummi tayi ta fama daita sannan tayi ta tsakura kmr wace ki tausayin abincin , yayinda muwaddat ba wannnan tarairayar take bukata daga garesu ba, ita makarantar ce batason zuwa ,tare da tunanin auwal. abi ne yasoma mikewa yana tamabayar muwaddat ko akwai abinda take bukata ?tace "abi kudin subcreb kawai nake bukata "ok zan sa ayi miki transfer ta dubu goma ai zai isheki? "yes abi nagode ya dubi ummi "to madam sai na dawo "ta mike tsaye ta d'auko briefcase dinsa suka jera kmr zasu shige jikin junansu tana gyara masa zaman hularsa , suna magana kasa kasa wanda hakan bai hana muwaddat jinsu ba, tabi bayansu da kallo kawai tana girgiza kai, su sam basa iya boye maitar soyayyarsu , ko cinye juna zasuyi oho? "gaban kowa nunawa juna tsansar soyayyar suke ,ta fad'i hkn aranta,ahankali ta ajiye spoon din hannunta tare da had'e hannunwata duka tayi tagumi tana tunanin rayuwarsu. adaidai bakin kofar fita ummi taja ta tsaya ta d'an rusuna tana mika masa briefcase dinsa ,yasa hannu zai amsa idanunsa akanta yace " nagode hubby, Allah yayi miki albarka akoda yaushe tsananin biyayyarki da kulawarki ke k'ara nusar da zuciyata cikin shaukin kaunarki wan... tayi saurin kai hannunta kan bakinsa domin katse masa hanzari tana yi masa alamar yayi shiru da maganar ... babu musu yayi shiru yayi murmushi yana yacigaba da kallonta "hubby plz ka daina min irin hk bby fa na kusa, " runtse ido yayi yana murmushi sannan ya karbi briefcase ya yayi gaba ta koma jikin window tana cigaba da kallinsa tana tsaye har sai da taga tashin motarsa sannan ta juyo tashege d'akinta kai tsaye, kinsa kanta ta sake yi ta fito adaidai lokacin da muwaddat ta mike "muwaddat kin gama ? "uhm kawai tace tare da gyara jakarta tayi hanyar waje ummi ta biyo bayanta har zuwa inda aka tanada domin ajiye motaci, da kanta ta bud'e mata gidan baya tashiga ta maida kofar ta rufe, tana k'ok'arin zagayowa direbansu ya k'araso da sauri yana gaisheta, ta amsa tashiga gidan baya ta zauna ya tadda motar suka fice daga gidan . akan hanyarsu ummi take sanar mata nan da sati biyu wata daya auwal zai dawo ,duk da taji dadi sosai amman sai ta dake tace "Allah ya dawo dashi lafiya, duk yadda ta dake hakan bai hana ummi fahimtar tayi farinciki da jin zai dawo ba, dan kallo daya zaka mata kasan tana cikin tsantsar farinciki ahankali ahankali ummi ta dinga janta da hira wanda daga baya ta dawo nasiha "muwaddat ki rike mutuncinki da namu, ki daraja kanki a makarata ki kame daga mugayen abokai, ki d'auki karatunki da daraja," dan Allah ina rokonki da ki maida hankalinki a karatu, domin yanzu kan maza ya waye fiyye da tunaninki ,akan auren mata masu mai ilimi har suka sauketa a makaranta nasihar ummi take mata . to babu laifi fad'an ummi ya d'an shigeta sai dai bata jin zata so karatu sama da aure, ita da zasu yi mata aure wallahi da sun gama mata komai arayuwarta, har taje ta dawo bata kiraM.A ba, kmr yadda bai yi tunanin kiranta ba, ta cigaba da sabgoginta *********** murtala international airport dake jahar lagos"cike yake makil da jama'a daga bangarori daban daban, wasu na sauka wasu na k'ok'arin tashi a cikin masu sauka wani hadadden matashi saurayi na hango yana saukowa daga matattakalar bene jirgi, kyau da kuma yanayin fatar jikinsa kawai zaka kalla kasan lallai kudi da hutu sun zauna masa ba karya, kayan jikinsa kuwa tun kan wando da rigarsa, takalmi har zuwa kan agogon dake d'aure da tsintsiyar hannunsa bana kasar Nigeria bane na kasar London ne , kallo daya zaka masa kasan komai dake jikinsa mai matukar tsada ne.. ahankali yacigaba da ta kowa har ya k'araso inda ahlinsa ke tsaye suna jiran k'arasowarsa, tun daya doso inda suke ta kasa d'auke idanunta akanshi saboda girman daya kara mai tattare da kurjini da haiba sam ba zakace d'an shekara 22 da biyu ba ne, kamshin turarensa ya sanya tayi saurin runtse idanunta sakamakon yanayin data tsinci kanta na zallar shaukinsa . lokaci daya taga yaja ya tsaya ya d'an juya kad'an yana yiwa wani matashi mai yanayin tsarinsa magana ,had'e da mika masa hannu ita dai bataji abinda suka tautaunawa ba har sanda suka saki hannun juna, matashin yayi murmushi sannan yayi wani bangaren daban, da alamun shima anzo tarasa ne, shi kuma ya nufo inda suke, yana gama k'arasowa abi da ummi suka shiga rigerigen isa garesa ummi ce tayi nasarar rungume shi ,kiss ummi ta fara yi masa all over his face tana cewa ya bunayya nayi missing dinka... ta fad'a tana kallon fuskarsa dake fitar da annuri kyau kmr shi ya halicci kansa sannan ya saketa rungume abi ajikinsa "you are welcome my lovely son "tkns dad i love you so much "bunayya duk ka canza ,ka ganka kuwa ka k'ara girma da kyau har kafi ni da abbanka kyau "ta fad'a cikin shaukin kaunarsa . bangaren muwaddat kuwa tana tsaye murnar ganinsa yasa ta manta da inda suke.. tsaye yayi byn ya gama da iyayensa ya hard'e hannunyensa duka ak'irji idanunsa akanta, kasa magana yayi yacigaba da tsayuwa har lokacin idanunsa na kanta yana kallonta fuskarsa cike da walwala da farinciki amman ita ta had'e fuskarta sosai taki bari annuri ya bayyana akan fuskarta ,wanda hakan yasa gabansa yashiga duka uku uku yana mamaki,ganin taki k'arasowa garesa sannan taki yi masa sannu da zuwa yasa murna dawowarsa ta koma ciki. ,ahankali ya dinga kallonta yana jin bugun zuciyarsa na karuwa ,shiru yayi yana kallon muwaddat da excitment is written all over yace "hummm tana kallona kmr bataji dadin dawowata ba,alhalin nasan itace mutun ta farko da zatafi kowa murnar dawowana, Muryarsa a tausashe yace "ke ba zaki min sannu da zuwa ba, kika tsaya kina kallona? tayi masa fari da ido sannan tace "baza'a yi ba, daka dawo ka kalli inda nake ?"ai ta ummi da abi kake yi ,me yasa kake tsammani zanyi maka sannu da zuwa, nunata yayi da yatsan hannusa yana murmushi "babu ruwana ummi abi kuna jinta ko, "babu wani muna jinta ai gsky ta fad'a inji cewar ummi "rabu dashi ummi wallahi yayi mugun rainane har da wani ce min ke kmr shi da sa'arsa "karka manta har yanzu ina nan amatsayin auntynka. aunty zaka dinga kirana ba wani muwaddat ko ke ba ,mara kunya kawai ta k'arasa mgnr tana murmushi ,bata kai ga rufe bakinta ba ya matso kusa daita sosai cikin fushi ya tsaya gabanta yana nunata da yatsa har jikinsa na tsuma yace "rainin kuma na nawa ? so nawa zance miki ki daina min kallon yaro, muwaddat ki daina ce min yaro...wallahi ki kiyayeni kina kirana yaro kmr ke kin haifeni ko kuma wata kanwar uwata, a filli zaka d'auka wasa yake amman ba zahiri 'bacin ransa a bayyane yake magana yake cikin 'bacin rai ganin kmr da gaske yaji haushin kiransa yaro datayi ,har yana neman da kusar da farinciki daya sauka dashi yasa tayi gaba tana tafiya had'e da cewa yaro kazo muje gida kasa mutane suna ta faman kallonmu . muwaddat .. ya kira sunanta taja ta tsaya batare da ta amsa ba yayinda ummi da abi sukayi murmushi"ai kun had'u kenan zaku dawo kmr karnuka .. suka nufi inda motarsu take, shi kuma ya k'araso inda take ya had'e fuska tare da matsowa kusa daita cikin yin kasa da murya had'e da tsura mata tsumammun idanunsa da suka sauya kala yace "muwaddat wallahi ki daina min kallon yaro nan .."kiji tsoron abinda yaron zai iya aikatawa " "me zakayi ,babu abinda yaro kmrka zai iya yi duk cika baki ne, ta sake juyawa yayi saurin janyota ya rike tafin hannuta cikin nasa yana massaging "ni nasan nayi miki yawa bazan miki kad'an ba, idan kuma kina mutsu ko a yanxu zamu iya gwadawa ,dariya tayi cikin d'aukar maganarsa shirme, ta sanya dayan hannuta ta zare hanunta dake rike cikin nasa sbd ganin yadda idanun mutane yayi musu ca aka suna faman kallonsu. domin gurin tmkr safiya ce sam bazakace dare bane saboda fitilun da sukayiwa gurin qawanya, tacigaba da tafiyarta ahankali hips dinta na juyawa cikin rausaya tace "kanina kazo mu tafi gida plz "shi kuwa tsumammun idanunsa ya tsurawa Hip's dinta tare da sauke ajiyar zuciya yana mai lasar lip's dinsa da hadiye yawu saboda ,tuni makoshinsa da lips dinsa sun soma bushewa, lokaci daya ransa yayi masefar bacci wani tuttukin bakinci ya caki tsokar dake makale da kirjinsa ganin yadda hankalin mazan dake gurin suka bita da kallo,ko bai fad'a ba yasan yabawa suke da kyawun surar jikinta wanda ko cikn hijab take sai anga yadda suke motsowa, cikin sauri sauri da zafin rai yabiyo bayanta ya bud'e gidan bayan datake zaune yashiga adaidai lokacin da direban su ammi yasoma k'ok'arin tayar da motar yashiga ya zauna yana cika yana batsewa direba ya ja. tunda yashigo motar idanunsa ke kanta yana kallonta cike da 'bacin rai "kanina kana son fushi dayawa wallahi, ka daina fushi irin haka saboda baya kananun yara matasa irin kyau, zai fi kyau ka saki fuskarka plz . bata k'arasa mganrta ba ya matsota sosai tayi saurin dubansa shima ita yake kallo kana yasoma magana cikin fushi "baki da kirki muwaddat sannan bakida tausayi.. naunauyen ajiyar zuciya ta sauke da karfin gaske sannan cikin siririyar muryarta tace "yanzu kuma me nayi daga dawowarka ? "komai ma kinyi dan girma allah me yasa kike min tallar jikinki? " Hip's dinki ... ta bud'e baki kenan zatayi magana tun bata soma ba yayi saurin had'e bakinsu guri daya.. dan yasan kalmar raini ce zata biyo baya Mmn sudais ce [12/23, 8:22 PM] +234 810 118 7859: 💗💗💗💗💗💗       MUWADDAT       💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗              ~NA~ *AYSHA  A BAGUDO*      ~DEDICATED TO~   _AUNTY SALAMATU AYYUBA_      _(UMMIN KADUNA )_ ~BEST AUNTY FOREVER AND EVER~ warning!!! don't read this novel  if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you   read it, is for   your own risk ..... WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim page 8 .....tsotsar bakinta yasoma yi ahankali  cikin wani irin salo na zallar shaukinta, cikin zuciyarsa yake jin wani irin sabon kaunar muwaddat na bin lungu da sako na gangar jikinsa, take joystic dinsa tayi wani irin harbawa tayi haniniya ta mike, bai san sanda ya janyota jikinsa ya kwantar daita bisa cinyoyinsa adaidai lokacin ya samu nasarar cafko laulausar harshenta, jikinsa har rawa yake ,ya manne bakinsa gam akan nata, yana wa bakinta wani irin tsotsa na fitar hankali,allah yasa  motar lemozin ce direba ba zai  iya hango abinda ke faruwa a baya ba, har suka iso bakin tafkeken get din gidan basu san sun iso ba, suna can duniyar tsotsar bakin juna.. ... ahankali direba ya sanya hancin motarsa ciki harabar gidan ,kai tsaye ya nufi inda aka tanada domin ajiye motacin gidan yayi parking ya fito, wanda tuni su ummi sun fito daga cikin motarsu suna tsaye jiran fitowarsu . ganin har tsawon minti biyar basu fito ba, yasa ummi k'ok'arin iso inda motar take parke ,  haka kawai ta tsinci kanta da jin matsanancin  fad'uwar gabar da batasan dalilinsa ba, gama isa ta ke da wuya ta kai hannuta jikin glass din motar da niyyar yin knowking, k'arar sautin wayarta ta karad'e gurin Wanda hakan yayi sanadiyyar katse musu hanzari ,   suka dawo cikin haiyacinsu , ita kuma ummi ta maida hannunta cikin jakarta ta ciro wayarta tana   duba screen din wayar ,sunan yayanta ne ya bayyana akan fuskar screen din, ta d'auki wayar ta manna a kunnenta"assalamu alaikum " daga can bangaren aka amsa mata da "wa'alaikis salam warahmatul ya auwal din ya sauka ko? "ya sauka lfy yaya yanzu ma shigowarmu gida kenan daga airport ta k'arasa mgnr tana kwankwasa glass din motar wanda yasa gabadayansu suka sauke naunauyen ajiyar zuciya suna kallon junansu kmr ranar suka fara ganin juna ,lumshe ido muwaddat tayi tare da d'auke  idanunta  cikin nasa ta maida kan sumarsa  kanshi data hargitse. jikinta a matukar mace ta kai hannunta ta gyara masa sumar kanshi kana tasoma k'ok'arin fitowa daga cikin motar ,yayi saurin rikota ya manneta da jikinsa sosai  zuciyarsa na wani irin harbawa "bari na rigaki fita tukunna, idan kika fita hk ummi zata  fahimci wani abu, lumshe idanunta kawai tayi ba tare tace masa komai ba, illa hannunta data kai kan joystick dinsa very slowly tana kwantar daita wanda kad'an ya rage numfashinsa bai bar gangar jikinsa ba .. alama tayi masa daya soma fita kmr yadda ya bukata, tana mai kawar da fuskarta gefe guda kirjinta na bugawa da sauri sauri, domin bata tanadarwa zuciyarta amsar da zata bawa ummi ba, idan ta tsareta da sankamammun tambayoyinta. ahankali ya kai hannunsa zai bud'e murfin motar , ummi ta sake knowking cikin d'aga murya "wai me kuka tsaya yi ne acikin mota haka? ",ku fito mana kuna 'bata mana lokaci magana yake son yi, amman yasan ko ya bud'e bakinsa  maganar bazata fito ba , kai tsaye yana gama bud'e murfin motar ya fito tare da gyara zaman rigarsa ummi ta tsura masa ido gabad'aya ta tsinci kanta da kasa d'auke idanunta akanshi ,yayinda shi kuma yayi saurin waskewa ta hanyar yin gaba abunsa yana shafa keyarsa ala'mun jin kunya , lokaci daya kuma yana bawa direban daya tukosu umarnin kai masa kayansa part dinsa, sannan yayi gaba ya isa inda abi yake tsaye suka jera tare zuwa cikin gida.. da sauri  ummi ta d'auke idanunta akanshi ta bud'e bangaren da muwaddat ke zaune wacce ta d'aura kanta bisa cinyoyinta kirjinta na wani irin mahaukacin bugawa daf daf.. , jikin ummi har rawa yake gurin cewa "bby me ya sameki haka ? "halan bunayya yayi miki sakarci  da rainin wayon daya saba ? "shiyasa fa kullun nake gaya miki ki rage shiga shirginsa bakiji magana , ta k'arasa mgnr tana d'ago fuskarta da hannuwanta duka "me yayi miki naga idanunki sun yi ja ..? murmushin karfin hali muwaddat ta kirkiro , tana yunkurin fitowa tace "kai ummi babu abinda yayi min fa, ni yanzu har akwai abinda bunayya zai min da zai dameni ,bunayya fa jina ne, koda yayi min wani abu ma bazan ta'ba bari ya dameni ba ,kaina ne dai naji yana d'an min ciwo" ummi ta sauke numfashi da ajiyar zuciya atare kana tace"kai wannan ciwon kan na rasa gane kansa wallahi , muje ciki ki sha maganin ki kwanta ,hannunta ummi ta riko suka nufi ciki suna shiga tayi hanyar up stairs daita  "ummi ina kuma zaku please ki dawo  bana son yin nisa dake i really miss you sweet mother "zan bawa bby magani  ta sha ,yanzu zan dawo nima nayi missing dinka ta fad'a cikin matsananci farinciki, murmushin gefen baki Bunayya yayi "gskiya ummi kina shabgwa'ba yarinyar nan dayawa shiyasa take raina mutane, ki rage shagwa'bata saboda ba lallai ta samu mijin da zai jurewa shagwa'barta ba. "karka damu zata samu da ikon Allah, ba mijin da zai jure shagwa'barta ba, mijin da jurewa komai na rayuwarta Allah zai azurta ta dashi, bunayya da abi suka kalli juna suna murmushi "ni dai ummi ki dawo tukunna ki zauna nayita kallonki nayi missing dinki Allah , karki biye mata, saboda  nasan babu  abinda ke damun wannan yarinyar zallar shagwa'ba ne kawai ke damunta, ya fad'a mata hk yana tsare muwaddat din da tsumammun idanunsa masu kashe mata sansar jiki ,  ko sauraronsa ummi batayi ba ta nufi d'akin, suna shiga ta zaunar daita a gefen gado ta bud'e durowanta  da take ajiye magungunata ta ciro paracetamol ta mika mata,sannan  ta k'arasa inda k'aramin fridge dinta yake ta d'auko ruwan roba ta mika mata "maza ki sha ki nemi guri ki kwanta ki huta, kar  bunayya ya takuraki . muwaddat ta yatsina fuska saboda bata son shan, magani " juya maganin tayi tayi a hannunta tana tunanin sha  ,   sai da ummi ta amshi maganin a hannunta ta 'bal'bala mata sannan ta sake mika mata ta sha, ta kwanta agefen gadon.   bata so kwanciya da shan magani  a daidai wannan lokacin ba, saboda tasan babu abinda ke damunta salon banayya ne  kawai ya hargitsata da yawa, amman babu yadda zatayi da ummi .   ahankali M. A ya mike ya nufi part dinsa ya shiga , komai yana nan kmr yadda ya tafi ya bari, koina tsaftsaf da alamun ma kullun sai an gyara part din "Allah sarki uwa kenan, uwa mai dadi,uwa mafi uba, duk wanda ya rasata yayi kuka, duniyar da babu uwa acikinta zallar kunci ne tattare da raunin rayuwa, ya fad'i hkn acikin ransa yana mai zama akan daya daga cikin kujerun dake  cikin part din,ahankali  yake  fitar da numfashin dadi "byn kmr minti goma ya mike yashiga ciki ya watsawa jikinsa ruwa ,ya fito ya tsaya gaban mirrow yana kallon fuskarsa zuwa wasu wurare na sansar jikinsa ,kirjinsa dake cike da laulausar gashi ya shafa zuwa mararsa yana lumshe tsumammu  idanunsa , sannan ya janyo daya daga cikin jakar kayansa da yazo daita ,ya ciro wasu  hadd'aun fararen kayan bacci ,ya saka ya dawo ya tsaya gaban mirrow ya d'auki man gyaran gashi daya zo dashi ya shafa akai. banda walkiya babu abinda gashin kansa yake, gyara fuskarsa yayi da hannuwansa tare da cewa "ya rabbi ga bawanka ya dawo da manufarsa tason yin aure ,Allah kasa iyayena su fahimceni su bani goyon baya,   ya fad'a hk sannan ya fita zuwa bangaren iyayensa . yana shiga parlour'n ya iske  abi da ummi zaune kusa da juna kamar zasu shige jikin juna suna kallon tashar CNN suna hira,, ummi na ganinsa tayi saurin mikewa had'e da ware masa duka hannuwanta ala'mun yazo gareta, cikin kasaita ya tako ahankali ya fad'a jikinta suka rungume juna, girgiza kai abi yayi yana kallonsu cike da so mara misaltuwa, "soyayyar uwa da d'a  na matukar burgeshi, he can't stop looking at them dan wani irin soyayyarsu yake jin acikin zuciyarsa, bai san da mai zai had'asu dashi a  cikin rayuwar duniya nan ba, muryarsa a tausashe yace " kulawar ta isa haka hubby , kar fa yazo yafi  sonki akaina, ki d'an rage wa abbansa  space , ya fad'i hk cike da zolaya yana murmushi "ki barshi yazo gareni nima naji dumin jikinsa " "zai zo ne amman kasan soyayyar uwa da d'a, ta wuce ... "ta wuce ta uba ba? "abinda kike son ki fad'a min kenan abi ya k'arasa mata mgnrta ,ta yi murmushi had'e da zare M. A daga jikinta tana shafa fuskarsa yarona kayi kyau sosai ,"jika gurinsa kar zuciyarsa ta buga . gabad'aya suka kwashe da dry, M. A ya k'araso gurin abi ya durkusa agabansa "i love both of you "babu wani banbacin atsakaninku, domin kune duniyata bani da wad'anda suka fi ku " abi ya numfasa yana hararar ummi sannan ya meida idanunsa kan tilon d'ansa yana jin farincikin dawowarsa "no sai dai ka zabi daya acikinmu inji cewar ummi "M. A ya tsaya yana kallonsu yana   duba ta in da zai ga fitowar muwaddat . abi yace "to ina jiran naji wanda zai zaba cikin ni dake ," bunayya kaji abinda umminka  tace" ka zabi wanda kafi so acikinmu, but karka manta ni uba ne wanda ya jibanci  al'amuran rayuwarka" "ni kuma uwace danayi silar zuwansa duniya ba.. ta fad'i hkn tana k'araso inda suke ta zauna, dariya sukayi gabadayansu, M. A ya zauna tsakiyarsu ya riko hannuwansu cikin tafin hanunsa "abi  ummi duk ina sonku fiyye da komai arayuwata ,samun iyaye irinku  na da matukar wuyar samu arayuwa ,ya k'arasa mgnr yana canzar akalar maganarsa da cewa "ummi ina muwaddat ne? "ina aunty'nka zaka ce ba muwaddat ba? ya shagwa'be fuska "haba ummi wai me yasa kike son maidani baya ne? "kowa yasan ni ne babba akanta  ,go slow dana samu ne aciki ya kawo tazarar dake tsakaninmu daita ammn  duk da haka nine yayanta .. "yanzu dai tana ina? ummi ta ta'be baki tace "Allah ya rabaka da son girma bunayya , ko gyanbo ya sara maka gurin son girma, kai ace da gaske ka girme muwaddat  ba'a san abinda zakayi ba. "wata killama kace "mu ma ka girmemu...... suka sa dry ita da abi suna dubansa, shi kuwa murmushin gefen baki yayi yace "haba ummi ai duk son girmana ban isa na goga daku ba ..... "kaga muwaddat tana d'akina ta kwanta kanta ke ciwo ,muje kaci abinci.. matse yatsun hannunta dake cikin nasa yayi  "ummi bari naje na kirata dan  abincin nan ba zai samu cuwu ba idan bata kusa dani ya fad'a yana mikewa tare da yin hanyar sama . suka bisa da idanu kawai suna kallonsa ,wani lokacin suna mamakin wasu abubuwa da bunayya ke yiwa muwaddat , masu  kama da wani bagire na daban, sai dai a wasu lokunta kuma suna ajiye hakan amatsayin shakuwa ce kawai mai karfi a tsakaninsu " "bunayya ummi takira sunansa ya tsaya cak yana juyowa adaidai tsakiyar step "ka dawo kaci abincinka kai kad'ai ka barta tana  bukatar hutu  "no ummi barin naje nima naga yanayin jikinta,dan  bazan iya komai batare dana nasan halin datake ciki ba, kinsa jini da tsoka ya k'arasa mgnr yana cigaba da taka step. abi yace "ki barsh mana yaje ya dubata ni kuma kinga sai ki samu damar dubani nima " "kai mai ya sameka da za'a dubaka? "komai ma ya fad'a yana dariya "wallahi hubbey ka rage wasu abubuwa girma kake yi ,dubi muwaddat da bunayya girma suke fa.. "ok girmansu yake nufin kar abani kulawa ko me? "a'a kawai dai ka rage wasu abubuwa ta k'arasa fad'ar hk tana driya da shafa sumar fuskarsa "ai kuwa zaki sha mamaki agidan nan idan kika daina bani kulawa " "mamaki kuma na me? "na aure mana ,zan nemo  k'aramar yarinya na aure  abuna .....  "ai kuwa daka burgeni wallahi ,ni har so nake kayi aure  ,bunayya da bby ma kad'ai sun isheka," "ni saboda muwaddat nake gujewa  auren,dan ta bunayya babu ruwana, "ai kuwa daka jawowa kanka a gidan nan, cikin driya yace "oho koma dai menene aure zanyi kuma da muwaddat zamu shawarta ,suka sa driya sannan suka cigaba da soyayyarsu mai had'e da barkwanci. M. A tsaye abakin kofar d'akin ummi har zai yi knowking sai kuma ya fasa yayi sallama ya tura kofar d'akin yashiga   ,batare da ya tsaya ayi masa izini ba, yana shiga  ya maida kofar d'akin ya rufe  ,ya isketa kwance tana latsa waya tana ganinsa ta yunkura ta mike zaune ta jingina bayanta da abun gadon ta runtse idanunwata kad'an sannan ta bud'esu, ta tsura masa tana kallonsa, yana takowa ahankali zuwa gareta, shima tsumammun idanuwansa ya tsura mata yana kallonta  ,sam bazaka ce M. A matashi ne dan shekara 22  ba saboda yanayin girman jikin da Allah yayi masa, komai nasa irin na manya maza ne ,fuskarsa ce kawai take bayyanar da kuruciyarsa a fili  . batayi yunkurin d'auke idanunta akanshi ba ,haka shima kallonta yacigaba da yi na wani lokaci sannan yace "rashin lafiyar kenan kin wani baje akan gado kina chartting  ? "oya miko min wayar naga da wakike wannan shirmen . "tayi masa shiru  har sanda ya k'araso ya zauna kusa daita yana shafa sumar kanta daya zubo gadon bayanta yana kyalli kallonsa ta sake yi " miko min wayar sannan ki tashi muje  naci abincin . sai lokacin ta bud'e bakinta cikin siririyar muryarta tace "kaje kaci abincinka ni a koshe nake  "me ki ka ci? "abinci tace masa ataikace   tana rausayar da idanunta cikin nasa. ya kamo laulausar tafin hannuta cikin nasa yana massaging ahankali ahankali,sai da yayi  kasa da murya sosai yace "muje ki taya ni ci, kinsa dai bazan iya sakawa cikina komai ba matukar bakya kusa dani ko? "wake taya ka cin abinci acan? "can daban nan daban, dan haka ki tashi kawai muje matukar kina son zaman lfy ya fad'i hk yana tamke fuska kmr wani babba hakan da yayi ,yai mugun bata dariya. "murmush kawai tayi tace "sannu yayana ko wani ubana har da wani had'e fuska kana bani umarni ..."yes ni yayanki ne kuma a wani muhalin zan iya d'aukar matsayin uba , domin abubuwa da yawa sun nuna hakan a zahiri "to ba zanje koina ba hutawa nake son yi..... "kinsa Allah ,wallahi sai kinje ,kin zauna tare dani naci abinci koda bazaki ci ba, idan ba haka ba.. .. "idan ba haka ba fa ,me zai faru? "ka fa dawo kenan zaka soma takurawa mutun, k'aramin yaro da kai sai son ikon tsiya da salo " bata ankara ba taji yayi mata wata irin fixga sai gata ta fad'o saman jikinsa ya matseta gam yana fitar da numfashi ahankali ,ya kai bakinsa daidai wuyanta yana lasar wuyanta zuwa dukiyar fulaninta take jikinta ya d'auki rawa mata,  sannan yace "wallahi ina gaya miki ki daina ce min yaro,  muwaddat ki kiyayeni da kalmar yaron nan da kike fad'a min kullun ... " babu yaro fa a halin yanzu a wannan duniyar , idan ma akwai shi to yana bayan uwarsa ,sai kiyita ce min yaro yaro kmr wata uwata "shekara nawa ma kika bani a duniya daza kiyita ce min yaro ? "ko second daya na baka a duniya na girmeka bunayya balle har tsawon shekaru uku zuwa hud'u, karka manta har pent na ta'ba saka maka ya had'e fuskarsa sosai tmkr wanda aka aikowa da sakon mutuwa sannan ya sake manneta da jikinsa  har kasusuwansu na tsarkewa da juna , ta bud'e baki zata saka k'ara yayi saurin had'e bakinsu guri daya yashiga sarrafa harshenta da hakoranta yana kallon cikin kwayar idanunta dake fitar da wasu kibiyoyi suna shiga cikin idanunsa, cike da mutuwar jiki ya sakar mata baki yana fesar da numfashi, cikin yin kasa da murya tare da d'an tsura mata ido,take jikinsa ya mutu ya lumshe ido  yace "bby ki daina raina shekaruna ki daina ce min yaro koda shekaru dari kika bani a duniya, ina jin haushin yaron nan da kike kirana dashi wallahi , kina min kallon yaro ni kuma ina miki kallon nayi miki yawa sosai , idan kuma kina shakku nan gaba zaki iya tabbatar da hkn... driya tayi cikin d'aukar maganarsa amatsayin shirme, tasan tana matsanacin sonshi ,amman bata tunanin zai iya sarrafata balle har ya iya gamsar daita " ka iya bakinka bunayya bakowace magana zaka dinga gaya min ba domin ni aunt..... tun kafin ta k'arasa ya sauke bakinsa ajikinta yasoma kissing din wuyanta zuwa kirjinta kafin kace me tuni kamaninsa ya sauya, haka itama tasoma fita haiyacinta. su ummi kuwa suna can suna jiran fitowarsu , sai daya d'auki kusan minti goma yana kissing dinta sannan ya sausauta rikon da yayi mata, ya yunkura daita ya zaunar daita akan cinyarsa yana kallonta "iya haka ma kin ji a jikinki ina ga ance mai gabad'aya za'a yi . ? zumbur ta mike tayi gaba domin batason taji abinda zai k'ara fad'a ya biyo bayanta yana kiran sunanta . "Allah bunayya baka da kunya ka rainani dayawa"yace  "to idan ban rainaki ba me kike son nayi miki ? saukowa sukayi gbdy jikinsu a sanyaye kmr wad'anda aka yiwa duka,  ummi na ganinsu ta mike da sauri  ta nufi dining tun kafin su k'araso tasoma zuba musu Whit rice da cowslow, muwaddat  ta k'arasa da sauri ta isa kusa da ummi "ummi kawo na zuba masa "bar shi kawai ya kan naki? ta rausayar da idanunta tana duban M. A dake tsaye hannuwansa duka zube cikin aljihun wandon  tace "naji sauki ummi sai dai wannan yaron na k'ok'arin dawo min da ciwon sabo .. yayi saurin kai hannunsa zai buge mata baki yana huci ta kauce  " ummi kina ganinsa ko " "wai bunayya me yasa ka raina muwaddat ne, byn ba sa'arka bace ? "to ki ce mata ta daina ce min yaro saboda ni ba yaro bane, ki gaya mata ko yanxu aka aura min irinsu hud'u zan zauna dasu ..." "no no bunayya kai din fa yaro ne girman jiki ne kawai.. ummi ta fad'a tana zuba miyar naman kaza a wani plet tana cigaba da mgn "banda abunka ina k'aramin yaro irinka yake da karfin auren mata hud'u? ko mahaifinka daya yayi tukunna, banza M. A yayi dasu ya ja kujera ya zauna sannan ya janyo plet din abinci ya soma cin dan idan yace zai yi mgn to wallahi zai yi katobara.. muwaddat ta kunshe baki da hannunta tana driya ta nufi gurin abi dake zaune yana musu dariya shima, shi kuwa tsaida cin abinci yayi, ya tsurawa bayanta ido tare da sauke ajiyar zuciya yana mai lasar lip's dinsa "ya rabi ka mallaka min wannan baiwar taka har ummi ta turo masa Fruit bai sani ba yana can gurin kallon bombom din muwaddat dake juyawa ahankali har sai data zauna sannan ya d'auke idanunsa, bawani cin abinci yayi ba saboda abinda ke damunsa yafi karfin abinci.    mike yayi  yasoma takowa zuwa inda take "muwaddat muje part dina kiga irin abubuwan dana zo miki dasu batare da mutsu ba muwaddat tace "ok ta mike ummi wacce ta kasa rufe bakinta tsabar farinciki tace "amman dai da ka bari zuwa gobe sai ka nuna mata akwai gajiya atare da kai yanxu , bugu da kari  gashi  dare yasoma yi ka duba lokaci kagani, karfe goma da wasu mintuna ta wuce. "murmushi yayi yace "ummi babu wata gajiya atattare dani, kawai nuna mata kawai zanyi ta d'auki wanda yayi mata sauran akaiwa su   ihsan ,"no bazata ba gsky Allah ya kaimu gobe  lafiya ta gani. bai sake cewa komai ba, yayi gaba , abi ya kira sunansa  bunayya yaja ya tsaya cike  da 'bacin rai "kuje amman kar ta wuce minti  goma ta dawo muna nan muna jiranku, yayi murmushin jin dadi ya kama hanyar fita yana fitowa bakin kofa yaja ya tsaya har sai data fito yace tayi gaba batasan dalilin da yasa duk sanda zasu kasance tare yake son sakata gaba ba . muwaddat na gaba bunayya na biye daita a baya yana kallon bombom dinta ,da yadda take motsasu ahankali cikin wani irin salon tafiya mai d'aukar  hankali . Mmn sudais ce [12/24, 2:35 AM] Hassan: 💗💗💗💗💗💗 MUWADDAT 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 ~NA~ *AYSHA A BAGUDO* ~DEDICATED TO~ _AUNTY SALAMATU lAYYUBA_ _(UMMIN KADUNA )_ ~BEST AUNTY FOREVER AND EVER~ alhamdullahi am back again. warning!!! don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you read it, is for your own risk ......wannan shine. WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim page 9 .....kafafuwanta suka hard'e saboda irin kallon kurrular da M. A yake binta dashi , amman duk da haka a natse tacigaba taku tana d'aga kafafunta ahankali , duk yadda taso ta kaucewa kallonsa ,hakan ya gagara . wannan tafiyar da take ahankali tamkar an tsamota cikin ruwa ba k'aramin sake tsuma zuciyarsa tayi ,saboda yadda jikinta ke moving da rawa , tana shiga parlour'n taja ta tsaya rungume da hannuwanta duka akirji tana fesar da numfashi tamkar wacce tayi gudun famfalaki . ahankali shima ya sanyo jikinsa gbdy cikin parlour'n, had'e da maida kofar ya rufe, har da sanya makuli, ya jingina bayansa da jikin kofar had'e da tsura mata tsumammun idanunsa yana kallonta , suna had'a ido kowanne ya kafe d'an'uwansa da kallo zuciyoyinsu na ayyana abubuwa da dama, bangarensa kuwa yaba kyawun surarta yake yi ganin yadda jikinta yayi matukar amsa doguwar rigar abayar jikinta,ta yane kanta da k'aramin mayafin rigar ,gashi daman irin karuwan jikin nan gareta masu d'aukar hankali. yadda ya zuba mata idanu ya kasa d'aukewa ,haka itama zuba masa ido tayi tana kallonsa batare da tace masa komai ba, illa kirjinta daya shiga bugawa da karfin gaske saboda ganin ya maida kofar ya rufe har da sanya key , shine ya katse shirun ta hanyar yin kasa da muryarsa tamkar mai jin bacci yace "wannan kallon fa kmr zaki cinyeni? ya fad'i hkn yana furzar da iska... rausayar da kwayar idanunta tayi cikin nasa kana ta bud'e bakinta da kyar tace "gani nayi ka rufe kofa alhalin hakan bai kamata ba " "uhmmm agurinki ne bai kamata ba ,amman agurina hakan shi yakamata, domin ni maji'bacin rayuwarki da al'amuranki ne, idan babu ni babu ke, haka zalika idan babu ke babu muhammed auwal .... ya karasa fad'ar hk yana zagayowa ya rungumeta ta baya ya matseta gam ajikinsa kamar zai maida ita cikin jikinsa . ta saki k'ara mara sauti tana k'ok'arin zamewa daga jikinsa saboda yanayin data tsinci kaina ciki mai wuyar misaltuwa, amman ta k'asa saboda sake rungumeta da yayi ajikinsa da iyakacin karfinsa ,yana busa mata iskar bakinsa mai tsuma zuciyarta "yau gani agabanki ,ki taimakeni ki furta min kalmar kina sona kmr yadda nake sonki fiyye da komai a duniya ,ki amince da kina sona ,ki daina kallon rashin dacewar kasancewarmu cikin inuwa daya, ina sonki muwaddat kuma a shirye nake dana mallakeki amatsayin matata ta sunnah , ki amince min plz, a yanzu hk burina bai wuce na nasarwa ummi da abi ba saboda nasan kema kina sona ... tayi saurin zaro idanu waje tana girgiza masa kai, ahankali ta juyo suna fuskantar juna had'e da shakar numfashin junansu, da kyar tasamu ta fixgo magana "bunayya ka ..ka daina tunanin ina sonka, irin soyayyar da kake tunani ba irinta nake ma ba, tabbas ina sonka muhammed auwal amman soyayya irinta 'yan'uwanaka, ka ajiye soyayyar da kake cewa ina maka a wannan muhalin " "abinda na tsani ji kenan arayuwata ,irin wannan soyayar sam bana bukatarta atsakaninmu "baby i love you, you won't understand how am feeling about you , ya fad'a yana sake had'eta da jikinsa, "wallahi na yarda ke aunty'na ce amman hkn nan na tsinci zuciyata da tsananin kaunarki " nasan kema kina sona muwaddat kmr yadda nake sonki dan Allah karki cutar da zukatanmu, idan baki aureni ba komai zai iya faruwa dani " "babu abinda zai faru da kai......sannan kar ka sake ka furtawa kowa wannan kalmar, asalima kasan burin iyayenmu akanmu na ganin mun samu ingantaccen ilimi mai zurfi kafin aure.... yawo yashiga yi da duka hannuwansa a sansar jikinta yana romancing dinta cikin salon wayonsa , wanda hakan yasa ta dinga jin jikinta na macewa da amsar salon dayake mata ,lokaci daya kirjinta yashiga dokawa da sauri sauri, dan wani irin tsoro ne ya ziyarceta , cike da sanyi jiki ya kamo hannuta ya nufi kan kujerar kushin, ya zauna tare da zaunar daita akan cinyarsa jikinsa na wani irin rawa "shikenan shikenan!! nasan da wannan burin nasu akanmu , zan hakura har xuwa sanda muka gama karatunmu,idan mun gama zaki aureni zuwa lokacin ? tayi shiru ta tsaida kwayar idanunta cikin nasa tana kallonsa kirjinta na dokawa da sauri , "ki daina min irin wannan kallon, yana matukar kashe min jiki, a duk sanda kika yi min " ki bani amsa kawai, zaki aureni idan kin gama karatunki nima na gama nawa ? haka kawai ta tsinci kanta da girgiza masa kai ala'mun a'a had'e da kawar da fuskarta gefe guda tana kallon d'akin "ba zaki auri muhammed auwal ba? ta d'aga masa kai ala'mun eh "to yaya kike son yayi da rayuwarsa me tattare da shaukin soyayyarki....? "hakuri ta furta hkn tana 'ko'karin mikewa tsaye daga kan cinyarsa yayi saurin kamota ya maidaita jikinsa "ki zauna bamu gama magana ba tukunnan "me yasa bazaki aureni ba? "saboda kai kanina ne ,ta tsinci kanta da bashi amsa da abinda ba shine a cikin ranta ba, taso ta amincewa soyayyarsa a wannan lokacin amman gabad'aya tarasa dalilin dayasa ta kasa furta hakan a zahiri ,sai ma hango kankantarsa data yi yanxu idan ya aureta me zai ce mata? tayiwa kanta tmbyr tana sake yunkura zata mike, wannan karon bai ce mata komai ba, haka zalika bai yi yunkurin tsaidaita ba, saboda takaicin maganarta. shiru tayi tare da tsura masa idanunta tana aika masa da wani irin kallon mai tadda sha'awa, kallonta kawai yayi ya lumshe idanunshi dan a yadda yake jin kansa, idan yacigaba da kallonta komai zai iya faruwa. ta yatsin fuskarta tace "ina tsarabar da kazo min daita ? "ka bani zan wuce kar ummi taga na jima ,ya nuna mata hanyar d'akinsa kawai da yatsan hannusa batare da yace mata komai ba, saboda bazai iya magana ba, koda ma yace zai yi sam sam muryarsa ba zata fito ba, gumi ne kawai yashiga tsa tsafo masa ta koina ajikinsa , gabadaya kwakwaluwarsa ta d'auki caji sakamakon d'acin kalmarta garesa . yana kallon yadda tashiga jujjuya jikinta tana takawa ahankali, yayinda koina ajikinta yake motsawa a duk taku daya daza tayi most especial hips dinta, cikin rausaya tashige cikin d'akin tana cewa " wlh bunayya ka maseefar raina ni ... yayi saurin d'auke idanunsa akan bombom dinta tare da sauke naunayen ajiyar zuciya yana lasar lip's dinsa saboda wani abu daya ji ya tsagar masa tun daga kwal'kwaluwar kansa har zuwa tsakiyar kafafunsa . ahankali ya runtse idanunsa har sanda ta fito ta tsaya a gabansa idanunsa a runtse suke, amman agaresa tar yake kallonta most especial kirjinta .... "bunayya ta kira sunansa cikin sanyayiyar muryarta me dadin sauraro da kashe jikin duk wanda yashiga kunnuwansa "banga komai ba, ni zan wuce idan zaka fito gobe kafito min dasu.. ta juya da niyyar barin d'akin ya riko damtsen hannunta sai gata agabansa tana yatsina fuska. ya Bud'e idanunsa dake runtse tar akanta yana kallonta yana girgiza kai can km yasoma k'ok'arin bud'e bakinsa,"i love you aysha......... .dan Allah ki soni mana kmr yadda nake sonki . bakinta na rawa tace" nagaya maka karka sake furta wannan kalmar ,gara ka canza wata, amman ban da wannan, sannan ka sakar min hannuna na wuce kana 'bata min lokaci .. "to bby nah me kike son na fad'a to byn wannan kalmar ? "ai duk abinda zan fad'a bai wuce wannan kalmar mahimmanci ba agurin , kawai ke dai, kin ki fahimtata ne kawai, sannan bakya fahimtar yadda na kamu da matsanancin sonki, Allah aysha ina sonki fiyye da komai, ina daya daga cikin wanda so yayiwa mugun kamu ,yake matukar yi musu rad'ad'i a zuciya, shiyasa ban so bayyana miki hkn ba , dan kina yi min abinda kika ga dama , kina careless da maganata, sam baki bata mahimancin daya dace" "Ai maganartaka ce Sam sam bata da amfani ,Dan tsabar rashin kunya ka dubi tsabar idanuna ka dinga gaya min kana so na ... "to meye acikin dan nace ina sonki muwaddat ? Ya katseta ta hanyar fad'ar hk yana tsareta da tsumammun idanunsa "meye dan na bayyana miki sirrin dake raina ? ,"ni kad'ai nasan yadda nake ji akanki aysha ina sonki kinsan da haka ,wannan tishi ne kawai da zuciyata ke sake miki .. "Azahiri ina hango rainin da kika min sai dai kisani al'amari na aure Sam babu raini acikinsa domin ni cikakken nmj ne Dana tattara duk wani muradin diya mace ,babu abinda bazan iya miki ba ..... Zaro idanu waje tayi tana mamakin zantuttukansa gareta ,kwayar idanunsa kad'ai ya tabbatar mata da gaske yake nufi, cikin sanyi jiki ta zare hannunta ta juya da niyyar barin d'akin dan gabad'aya maganganunsa kunya suke bata . "aysha.....ya kirata yana maida bayansa ya zauna sosai yana ware kafafunsa, kmr jira take ya kirata ta tsaya cak batare da ta juyo ba, saboda yadda kirjinta ke dokawa "ki samu natsuwar zuciya tukunna kafin ki fita daga d'akin domin matukar kika fita haka tabbas zaki fallasa abinda ke cikin zuciyarki .. Juyowa tayi cikin had'e fuska tana hararasa "ka fita idona Auwal banason wannan salon naka ,kai keda da zuciyata ko ni ? Abinda kake nufi ne dai bazai yiwu atsakaninmu ba kai kanina ne ni yayarka ce.. "Misali idan zan kasance yayanki zaki yarda ki amincewa aurena ? "Me zai hana ta bashi amsa da hakan .. "To ki yarda kina sona kawai ..."bana sonka! bana sonka!! kuma karka sake nusartata da wannan zance aikin baza kawai ,yaro k'arami da kai sai shegen fi'ili da manyance tsiya , ko ni guda nawa nake ballanatana kai? "ni wallahi har mamaki karfin halinka nakeyi. "ka girma a idanuna ka bud'e idanunka ka tashi ka ganni acikin gidan amatsayin yayarka Amman tsabar rainin hankali irin naka ka rasa wace zakace kana so wai sai ni .. "saboda kece irin type Dina shiyasa ,dan nasa irina ne kawai zai iya gamsar dake ,sannan ko mahaukaci ya kalli cikin kwayar idanunki zai tabbatar da kina son muhammed Auwal ,wai me yasa kike ganin kmr ba zaki iya aurena ba ? ta rausayar da kwayar idanunta cikin nasa tace "Saboda kamin kankata kuugunka yayi min kad'an bazai iya ... "Zan iya yin komai da kike tunani, ki cire wannan tunanin bby acikin kwakwaluwarki, wallahi tallahi bby kinji na ratsen miki zan iya yin fiyye da abinda kike tunanin , duk wani abu da cikakken d'a nmj zai yiwa mace ta fannin auratayya tsaf zan iya "wannan abar zai iya cika mararki har ma ya saura ya k'arasa mgnr yana sake yin balance da kafafunsa yana shafa saman mararsa. a matukar firgice take kallonsa kafin daga bisani muryarta na craking tace "ni.. ni din Auwal ? idanuwansa ya D'an lumshe mata kad'an yana d'age mata girarsa daya "kina mamaki ne ? "Idan kina mamaki nr wallahi ki cire hakan acikin zuciyarki,tabbas muhammed Auwal yaro ne, Amman ba irin yaron da kike tunani ba, dan siffarsa da halittar jikinsa ta bambamta data sauran yara mazan da kika sani "wannan auwal din daban yake, idan kuma har yanxu kina ganin yaro ne ni sai mu gwada abambance .... ta janyo numfashi da kyar ta fesar tace "wallahi yau na sake tabbatar da ka rainani ,Amman duk laifina ne, daman kuma ummi tasha gaya min sakewar danake maka tayi yawa.. mikewa yayi ya D'an tako zuwa inda take tsaye, ya matsota sosai kmr zai shige cikin jikinta taja baya da sauri, ya sake matsota sosai ta yadda babu yadda zata iya matsawa, cikin rad'a yace" ayshatul muwaddat karki manta kece kika fara fitowa da salon rainin daya girmama a zuciyar auwal "ke wallahi bama ki isa ba,sai kin amincewa soyayyata dole ,karki manta abubuwan da sukayita faru atsakaninmu a baya, idan ya 'bace acikin momery dinki ,ni yana nan kallonsa nake kmr a yanzu abun yake faruwa , ya k'arasa mgnr yana sausauta muryarsa sosai tmkr zai saka mata kuka "kece fa kika koyar dani yadda zan soki ,ban manta komai ba, komai yana cikin kwalkwaluwata, Auwal bai San komai ba sai da kika koyar dashi yadda zai yi ,kece da kanki kika koya min yadda ake shan baki da saffara kirjin mace ,tun babu komai akirjinki nake sarrafasu da tsotsarsu, na tashi da burin mallakar duk wata diya mace mai irin surarki, sai dai duk zaman danayi a kasar waje banga mai kayan dadi irin naki ba, saboda me bazan nemi haukace miki ba ? "wallahi matukar baki bani had'in kai ba za'a jimu a gidan nan ,kowa zai ji mu dake .. Matsawa tayi baya ta manne da bango sosai ya sake matsota har numfashinsu na gauraya take jikinta ya kama rawar , tana masa wani irin duba hankalinsa a tashe , yayinda zuciyarta ta cika makil da mamakin zafafan zantuttukansa akanta, lallai ta tafka babban kuskure arayuwarta, yau ita Auwal yake fad'awa wad'an nan zantuttuka ? " yaron da'a saninta shiru shiru ne, ma'abocin rashin son magana da kula mutane ,domin ita kanta ba kasafai yake shiga lamarunta ba, a tun sanda ya girma abubuwan da suka faru abaya ne suka shiga dawo mata cikin 'kwal'kwaluwarta ,shi kuwa cikin murya mai cike da kasala yace "kina mamakina ko ? "Ki daina mamakina muwaddat kece kika fara ni kuma zan d'aura daga inda kika tsaya domin cika burinmu, ya kamo tsintsiyar hannunta ya d'aura daidai saitin zuciyarsa dake dokawa "kinji yadda zuciyata take bugawa akanki ko ? "wallahi soyayyarki ce acikin zuciyata ba zallar sha'awa ba, ni dake jinsinmu daya ,kece macen dazata jiyar da Auwal dadi duniya, na hanga na hango banga macen da nake ganin zan samu natsuwa atare daita ba sai ke ,kece kawai zaki jiyar dani dadin Da nake bukata , saboda nasan zaki fi kowace mace dadi a duniya ...... "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ta furta tana sauke Ajiyar zuciya da karfi, tana mai fixge hannunta da karfi ,muryarta cike da in... ina tace "ma..mara kunya kawai ,wallahi Auwal baka da kunya . "to muwaddat ke zan ji kunya ...?ya fad'i hk yana sake matsota ya had'eta da kirjinsa muwaddat ta lumshe idanunta tana jin yadda numfashinta dana M. A ke gauraya yana k'ok'arin had'e bakinsu taki yarda "banson iskanci fa Auwal, wanda kayi d'azu ma kyaleka kawai nayi dan babu yadda zanyi da kai ,kai ban san abinda yashiga tunani ba da har na barka ka sha bakina ..... "ai dolenki kibarni na sha tunda soyayyata na yawo a jinin jikinki, kuma ma ai kece kika koya min ,ta yaya kike tunani hanani yanzu ? kema kinsa ba zai yiwu ba wallahi. "zan had'aka da ummi fa" "da kin taimakawa rayuwarmu domin nasan zatafi bawa maganar mahinmmaci ,sbd daga ni har ke muna tsananin bukatar juna ya fad'i hkn yana toshe mata hanci .. "wayyohlly Allah zaka kasheni ne? "wayyo numfashina , wani iri nake ji ajikina idan ka ta'bani ,dan Allah karka sake shan bakina... "karki damu yana da kyau kema ki ji irin abinda nake ji ajikina akanki ,ki san ba k'aramin k'ok'ari nake yi ba ,tsawon shekaru kenan ina fama da muguwar sha'awarki da soyayyarki ,wanda kece silar hadasa komai yana gama fad'ar haka ya lumshe idanunsa tare da had'e bakinsu guri daya yashiga tsotsa lip's dinta yana shafa gefen fuskarta da hannuwansa duka ,yadda yake tsotsar lip's dinta haka joystick dinsa ke mikewa ,tasoma k'ok'arin kwace bakinta "wayyohhly Allah muwaddat karki yanke min jin dadi , ya sake had'e bakinsu guri daya ahankali yake tsotsa lips dinta har yayi nasarar bud'e bakinta ya zira harshensa cikin bakinta tare da danna hancinta babu yadda ta iya haka ta kama harshensa tana tsotsa kmr tasamu sweet . shi kuma yana yawo da hannunsa a gabad'aya ilahirin jikinta tun tana turjewa har ta sadaukar gabadaya ta sakar masa jikinta,yashiga romacing dinta son ranshi ,tabbas Auwal daban yake acikin maza, kmr yadda yasha gaya mata domin babu yadda zata iya kwatar kanta daga garesa ,jin al'amun yana son kai hannunsa kirjinta yasa ta kamkameshi ajikinta ta manne kirjinta danashi Wanda kad'an ya rage numfashinsa bai bar gangar jikinsa ba ,ajiyar HRT yashiga saukewa . muryarta a sarke tace "Dan Allah ka barni haka ..ka barni !! na wuce ummi zata ... Idanunsa dake yawo a jikinta yasa tayi saurin d'auke numfashi ta kasa k'arasa mgnrta tana haki "iya haka ma kin ji ajikinki, dan haka ki daina rainani bby wallahi nafi karfinki, jarabata tafi karfinki za'a tara maza d'ari kafin kisamu mai irina halitatta, Dan haka ki daina min kallon yaro dan ni ba yaro bane .... Yana gama fad'ar haka ya saketa ya fad'a cikin kujera mai zaman mutun uku yana sauke ajiye zuciya, tsaki taja.. abinda tasan yafi tsana kenan arayuwarsa ,tun ba yau ba ya sha mata Gargadi akan tsaki. "karki sake yin tsaki nan ya fad'a yana tsura mata ido "me zakayi idan an sake ? "Ke dai karki sake ,kinsa sarai babu abinda ke saurin 'bata min rai kmr tsaki, rufe bakinsa ke da wuya ta sake yin wani ai kuwa ya Mike a harzuke yayo kanta yana shirin cafkota .... kafin kiftawa da bismilla ya nemeta ya rasa kmr wata iska , yarasa yadda akayi ta 'bace tsalle tayi, 'bacewa tayi shi dai bai sani ba sai nemanta yayi rasa ,aiko yace me zai yi ba dry ba yashiga dariya "matsoraciya kawai da kin tsaya kinga yadda zanyi dake ,ita kuwa tana bayan kujera jikinta na rawa . ahankali idanunsa ya sauka akanta "ki fito ki wuce karki sa ummi ta biyo sahu ,taki fitowa har sanda taji ya koma ya zauna,ta mike jikinta na kyarma ta bud'e kofar ta fita da sauri .. A bakin kofar part dinsa ta tsaya tana haki tana sauke ajiyar zuciya cike da matsanancin mamakin kanin nata, a yau yazo mata da abubuwa masu cike da ban mamaki da firgita zuciya, Wanda ya haddasawa zuciyarta shiga rud'ani ,tsawon minti goma tana tsaye agurin sannan ta nufi bangarensu ta tura kofar parlour'n tashiga tana sanya kanta ciki ,da ummi da abi idanunta suka soma cin karo suna k'okarin shiga d'akin kmr zasu shige cikin juna , atare suka juyo suna dubanta a tsanake ummi tace "yauwa bby kin dawo ? Muwaddat ta d'aga mata kai alamun Eh. "Okay ki rufe koina ki je ki kwanta,ahankali muwaddat ta juya da niyyar rufe kofa, su kuma suka k'arasa shigewa d'akin .. Tana shiga d'akinta ta fad'a Kan gado ta kamkame jikinta guri daya tana shakar kamshin turarensa ajikinta ,tana sake mamakin karfin hali irinn nasa, ko cikakken minti goma batayi ba kiransa yashigo wayarta ta d'auka daga kwance datake, ajiye zuciya ya sauke yana buso mata hucin numfashinsa yace "bby ki hau online plz " me kuma zan maka nifa bacci nake ji ? "Ni dai ki hau kawai ko nazo na sameki ,tasan halin nacinsa bazai barta ta huta ba, Dan haka tace shikenan zan hau, ya katse kiran ,ita kuma tayi kwanciyarta tare da kashe wayar gabadaya,tasanyawa kofarta key. Har kusan karfe dayan dare yana contact dinta Amman bai ga alamun zata hau ba hkn yasa ya hakura ya kwanta .. ********* Washegari a sanyaye ya shigo parlour'n bakinsa d'auke da sallama, ya iske abi zaune cikin tangameman parlour'n, wani k'aramin tebur ne agabansa mai cike da kayayyakin kalaci, dagin soye soye da ababen sha iri iri alamar bai dade da yin breakfast ba, tunda ko kwashe kayan kalacin ba azo anyi ba ,yayinda gefensa na dama muwaddat ce zaune tana kallo zeeword tana kur'ban ruwan shayi ,abi ya d'ago ya dubi tilon d'ansa cike da fara'a da sakin fuska sannan yace "ya'akayi ne bunayya me kake yi har wannan lokacin acikin part dinka har mun gama breakfast? lumshe idanunshi kawai yayi yace "babu komai ban tashi da wuri bane ya k'arasa fad'ar hk tare da cewa " gaida abi sannan yasamu guri ya zauna a yana fuskantar muwaddat ,abi ya amsa "ka tashi lfy ya gajiyarka ? "alhamdullahi bari auntynka ta had'a maka abun kari ko? kai kawai ya iya d'aga masa ya gyara zamansa yana canza cheenal. ahankali ta mike "me zaka ci? "ki bani abinda kika ce ya fad'a batare daya dubeta ba itama bata sake cewa komai ba tasoma had'a masa ta tura k'aramin tebur gabansa ta kwashe sauran plet ta nufi kitchen. tana barin gurin ya maida idanunsa akan mahaifinsa "abi ya furta muryarsa can kasa kmr mai koyan magana "ya'akayi ne bunayya, kana bukatar wani abu ne? "ko abincin ne bai yi maka ba? "uhmm komai yayi ai ummina daban take acikin matan africa gurin girki she's perfect abi yayi murmushin jin dadi an yabi masoyiyarsa. "abi ina son muyi wata mgn mai mahimmanci da kai wanda ya shafi bangaren rayuwata "to ka gama breakfast din mana sai muyi "no abi bazan iya sakawa cikina komai ba matukar ban amayar da abinda ke cikin raina ba" abi ya numfasa yana gyara zamansa "to ina sauraronka "M. A yayi shiru yana tunanin ta inda zai fara "abi ya tsareshi da idanu "ina sauraronka ka fad'a min damuwarka duk da bana tunanin wata damuwa ce mai tsanani "gsky abi nima a tunani bawata damuwa bace matukar za'a fahimceni daman dai aure nake so nayi acikin lokacin nan, idan ma da hali ina son kafin na koma hada Master's dina nayi ,na wuce tare da *matata* ...... abi yayi shiru yana kallonsa tare da sake maida hankalinsa gbdya akansa "aure nake son nayi acikin lokacin nan,idan da halima ina son na wuce da matata ya maimata hkn a kasan zuciyarsa yana cigaba da kallonsa . M. A ya d'an yi murmushin a kunyace yace "Allah da gaske abi ina son nayi aure naga ya'yana tun ina da karancin shekaru, shiyasa na dawo adaidai wannan lokacin kaga yanzu na had'a digirina na farko ina da karancin shekaru ,ina son kafin nayi join din master inyi aurena na huta .... ajiyar zuciya abi ya sauke da karfin gaske yana dubansa wanda zuwa lokacin muwaddat ta dawo parlour'n ta isa inda M. A yake ta d'auki remut ta koma mazauninta adaidai wannan lokacin abi yace "duk naji bayaninka amman nafi son ka kammala karatunka gabadaya sannan aure, yanzu ma da kake maganar aure kasamu wace kake so ne ko dai kawai auren zakayi? ya d'an yatsina fuska "ni dai dad'y ka amince min ina da wacce nake so ayanxu hk muna tare da ita muwaddat tayi saurin d'agowa tana kallonsa a matukar tsorace kafin ahankali tasoma girgiza masa kai ala'mun kar yayi mata hk.. "wace anan din? "nan dai daga ni sai kai sai kuma auntynka muwaddat ,ko acikin 'yan aiki kaga wace kake so ne? yayi murmushi kawai yana nuna muwaddat da bakinsa a tsoroce abi ya waigo gefen da take zaune , take tashiga girgiza masa kai "Allah abi wasa yake maka ... abi yayi dry "kai bby manya meye na saurin tsorata hk "abi ba tsoro bane ta yaya ma zaice ni yake so nifa auntynsa ce "wannan kuma gsky ne bunayya kayi saurin ido dayawa ,nasan da wasa kake yi ,idan ma gaske ne kabari ka kammala karatunka alabashi sai kayi auren... nan take abi ya shashantar da zance ya maida maganar shirme" ina M. A ina aure a yanxu duka guda nawa yake da zai takalo aure ..? wata hirar suka shiga yi yayinda shi kuma ya rasa abinda zaice yayi tagumi kawai yana dubansu " tunanin mafuta yashiga yi, yasan tunda mahaifinsa ya shashantar da maganarsa ko umminsa taji itama hk zatayi dan ra'ayinsu daya.. yunkura yayi ya mike tsaye zai bar parlour'n batare da yaci abinci ba "abi ya kirasa bunayya ya ba kayi breakfast ba? kasa cewa komai yayi ya tsura musu ido kawai can kuma ya juya ransa a 'bace ,abi yashiga kiran sunansa amman sam yaki juyowa cikin haka ummi tashigo parlour'n da sallama tayi wani irin azababben kyau sai kamshi ke tashi ajikinta "abi ya amsa yana kafeta da idanunsa kyawunta na nan har lokacin kamaninta bai canza ba sai dan manyanta datayi amman dayake ma'abociyar kwaliyace bamaza'a ce itace ta haifi M. A ba d'an kiba kad'an tafi muwaddat "hubbey lfy naji kana kiran bunayya cikin d'aga muryar da ban saba jinka dashi ba lafiya ? saurin waskewa abi yayi ta hanyar cewa "babu komai hira muke da muwaddat kunnenki ne dai yaji yo miki hk" tayi murmushi "to hirar me kuke yi?. "daman shawara muke yi da bby akan zanyi miki kishiya, wai ita tagaji da zama da aunty daya acikin gidan nan ummi tace uhmm "ka dai fad'i gsky babu ruwan bby idan ma dai auren kake so kayi ka daina kameme tun yanzu gara ma ka fito fili ka fad'a mana idan ka hango wata ne.. Mmn sudais ce