[07/11 9:03 pm] ★~AMMEY LAYLERH🤫: *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 1&2 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ _012/09/2024_ ❤🔥 BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM # OF THE LAW # A TAITOR's # ROMANCE # BLOCKBUSTER # A SOLDIER's # Courage # Hop0 # Is Crime ❤️❤️❤️❤️❤️ A duk loƙacin da Allah ya ƙaddara wanzuwar hallitar ɗan adam a doran ƙasa, to kuwa tabbas ko ya ƙi ko ya so akwai waɗansu tarin Ƙaddarorin da suke yin jerin gwano a gangar jiki da kuma ruhin ko wanne bawa, Inuwa wata aba ce da Ubangiji ya ke ƙaddara wanzuwarta manne a jikin kowanne abu, walau mai rai ko akasin haka... A kodayaushe tana bibiye da mune matuƙar bawa zai zuba maganansa zai lura da haka. Kalmar ƙaddara! Kalma ce mai ɗauke da rassa biyu walau ƙaddara mai kyau ko kishiyarta. Ƙaddara abokiyar tagwaitakar inuwa ce domin bawa ba ya taɓa shallake ma tarin ƙaddarorinsa, Duk iya gudun ka duk iya saurinka baka isa kujema tarin ƙaddarar da ubangijin sammai ya ƙaddara maka ba, sanin haka ya sa na fahimci karin maganar Malam bahaushe ta _Tun ran gini tun ran zane_ ta zauna ɗaram kwatankwacin yadda ake ɗora ƙwarya a gurbinta. Yau gani a matsayin matar aure wacce zata ci gaba da amsar wannan sunan har zuwa numfashina na ƙarshe, tafiya me zurfi ce ta kaimu wata anguwar da bansan ko wacce anguwa bace domin zuwa loƙacin na shiga kukan gasken. Tsaiwar da motocin sukayi ne yasa na fashimci mun kawo gidan su salman kenan, dan kuwa bazan ƙira shi da gidana ba. Hajiya Umma ce ta dafa kafaɗuna tare da faɗin. "Ki fito da ƙafar dama tare da bismillah Maryama" Wasu hawayene masu ɗumi suka sake wanke min ido shikenan ta tabbata kenan wayyo allah rayuwa na faɗa a cikin raina ina jin wani raunin dake son ɓallowa daga can ƙasan ƙasan zuciyana. Fusgar hannuna da naji an yine ya sanya ni ambatar sunan Allah a saman laɓɓana. Muryar gwaggo naji tana ruwan masiyar wai zaman uban me nake da har yanzu bazan fito ba, ko dan naga mota me kyau shine na maƙale. Allah sarki ita motar ta dama domin ni a loƙacin kukan tausayin kaina da kaina nake yi, ta sabuwar rayuwar da ƙaddara ta sake buɗe min sabon babinta. Wannan kyakkyawar dattijuwar ta ɗazu itane ta ceceni daga masifar gwaggo ta hanyar kama hannuwana zuwa cikin nata tafin hannun. "let go to ur forever home by grate of god" Ta faɗa a loƙacin da take shiga dani mahaukacin ƙaton get ɗin gidansu salman..... Haka suka shiga dani kaina a lulluɓe ina share ruwan hawayen da yaƙi tsayamin har zuwa loƙacin, tun a farkon shigarmu gidan na fara jiyo ihun ɓaɓatun gwaggo nata yaba gidan. Kuma ni kaina shaidar hakance ko daga yanayin yadda gidan ya ɗau haske tare da wani abu me laushin tsiya da naji ƙafana suna nitsewa a cikinsa. Amma duk hakan baisa naji wani abu daban akan auren ba haryanxu illama kalaman Anne da sukemin yawo a tsakar kaina shin me kalamanta suke nufi? Shine kawai fassarar amsar da nake nema a haukace ido rufa. Tunanina ne ya tsaya a sadda muka kai ƙofar shiga palon gidan, wata sabuwa kenan domin tuni ɗakin ya hautsine da maganganu jama'a kowa na tofa albarkacin bakinsa game da gidan. A falon aka zaunar dani wai wurin kakar ango a karan farko kenan da na ɗan ji mamaki, dan nasan dai salman baya da kaka a shegen surutunsa ya taɓa faɗamin shi baima san kakarshinba sai a photo ya santa. (Mebi ta ɓangaren Maman shine) na faɗi a raina ina ƙarasa zaunawa abinda ya sake kullemin kai shine yadda matar da suka ƙira da kakar ango itama ta amshemu a mutunce cike da girmama naji suna gaisawa da hajiya umma. Hannuwana naji an kama hakan ya tilastamin ɗago kaina don ganin ko waye. Idan nace mucu saida brain nawa ta juya karkuce nayi ƙarya domin a fusge sai naga face ɗin kyakykyawaer farar dattijuwar yamin kama da face ɗin dana taɓa sani a rayuwata. Saidai na manta inane a kuma ina hakan yasani risinar da kaina ƙasa ina jan ijiyar zuciya. Ganin yadda itama ta kafeni da nata idon. Dafa kaina tayi fuskarta ƙawace da kyakykyawan murmushi ta furta "Masha Allah da wanzuwarki a cikin tsatsona Marayma" Daga nan ta shiga kwararomin adda'oi su kuwa sauran ƴan kawo amarya tuni sun bazu a cikin gidan da naji anacewa ba anan zan zauna ba. Kana kuma abu mafi ƙara ɗaure kaina shine yadda naji Wannan matar tana waya tana cewa gobe Insha Allah jet ɗinsu da wari zai tashi, nan na shiga tambayar zuciyana dama su salman ɗin ba ƴan nan cikin lagos bane?, to amma kuma duk wanda yasan Isa manu a garin na lagos ya sanshi, bisne tambayar nawa nayi a zuciyata don bana da mai bani Amsarta. Tunanina ya katsene loƙacin dasu Hajj Umma suka firfito zasu tafi zance suke yi a juye wanda nidai ban gane masa. Domin ji nayi suna mata sallama suna cewa allah ya saukemu lafiya, su maman Abdalla sai wani yatsine yatsinen fuska ake. Domin makusa suke nema tako ta ina amma sun rasa. shi ya sanya suke wani huhhura hanci sama domin ba haka sukaso ganin rayuwana ta gyaruba, saidai basu sani ba duk abinda zai faru bawa rubutaccene tun daga rabbi izzati. shine yake tsara mana duk wasu tarin ƙaddarorinmu tun kamin muzo duniyar. Tunani ya sake katsewa ne a karo na biyy loƙacin da Hajiya umma take faɗin. "To _FULANI_ mu zamu koma ubangiji Allah ya basu zaman lafiya Ku kuma Allah ya sauke ku lafiya ita kuma yasa gidan zamane" (Ba ameen ba) na amsa a zuciyata. "To Merrah mukam zamu tafi duk abinda aka tsinta a gidan aure ɗan haƙuri ne domin kowa da haka yasa ba, barin m aure irin naki da babu ango babu dangin ango, Sai aje ata haƙuri da zaman haƙuri" Muryan ummansu yaya Ibrahim ya doki ƙofofin kunnuwana, ban gama dawowaa daga suman wucin gadin dana tafi ba na kuma tsinkayar muryar Matar da ake ƙira da fulani tana mai bata amsa ta cewa. "Kwarai kuwa zaman aure ɗan haƙuri! Rashin ganin ango ko danginsa kuma karki damu wata rana zaki sani domin mutane masu daraja ba a arha ko a sauƙi ake samun ganjnsu ba! Amma karfa ya zame miki wani abin damuwa very soon zaki sanshi harma ki ganshi, domin shi kamar walƙiya yake yanzu nan ƙya ganshi yanzu nan ya ɓacema ganinki don haka ki kasance cikin shiri da tsammani domin Malam bahaushe yana cewa _TSAMMACI ABINDA BA BAKA TSAMMATA BA_ don haka ki riƙe kalmar daram aranki inba da magoya bayinki saisu tayaki riƙe kalmar" Kafaf palon kowa tsayawa yayi yana kallon wannan dattijuwar matar ciki kuwa harda ni, bazance kaina ya kulle ba domin dama a kullen ake saidai gabana daya shiga dukan tara tara bama uku ba. Na shiga uku ni merrah Auren nawa ne kuma yazo min haka ajuye tamkar amaryar buzuzu. Ɗaya bayan ɗaya suka ringa ficewa motoci na ɗibarsu suna mayar dasu. Inaji ina gani haka a gaban idona kowa dazan ƙira da nawa ya tafi ya barni a wannan juyayyan gidan. Babu dadewa da tafiyansu matar farko da taje ɗaukana ta kama hannuna tana me kaini wani ɗaki wai anan zan kwana, baki ɗaya jikinane ya sake mutuwa mayafina na zame bayan fitar tana me sake tunasar dani tafiyar sassafene a gabanmu goben. Toilet na faɗa domin inada buƙatar sake watsama jikina ruwa kodan zafin da aka haɗama kaina. Har wani hayaƙi² ne ke fita a kaina tsabar zafin daya ɗauka... A ƙalla na ɗauki Good 30 minutes a bathroom ɗin kafin na fito ɗaure da Alwalana kayan dana cire na mayar tunda ina da tabbacin banda ko tsinke a gidan. Amma ga mamakina kodana fito sai na tarar da wasu riga da wando na barci masu kauri tare da madarar shanu me zafi, (Ikon Allah baya ƙarewa) na faɗi a zuciyata domin kuwa shi nake ta gani sai gashin zabbin da suma aka ajje duk akan table ɗin dake gaban gadon. Saida nayi nafila tare da adda'oi masu ɗan tsayi kana na janyo plat na naman domin ba karya sammm bana wasa da cikina, tak na tafe cikina da gashin naman nan na kora da madarar shanun me dumi sosae. Adda'ar kwanciya barci nayi ina shirin kwanciya fulani ta shigo dana rike sunanta daram.Tambayana tayi babu abinda nake da bukata nabata amsa da babu kana taja min ɗakin tana me fita,Wata sabuwa kuma tana fita na rushe da wani sabon kukan na sabuwar rayuwar dana tsinci kaina wadda ƙaddara ta kawoni izuwa wani matakin na daban. A haka har bansan tsawon loƙacin dana ɗauka ina kukanba haka bacci yayi awon gaba dani fuska fall burbushin hawaye. ƙiran sallar farko a kunne na haka na yunƙura na tashi inda na tashi da wani zazzafan zazzaɓi da ciwon kai wanda nasan kukan jiyana ya haddasa min zazzaɓi da ciwon kan. A wahala nakai kaima bathroom na yo alwala da nafila na fara ina nan zaune har aka shiga sallah nima nabi sahu nayi. Kaɗan garin ya fara haske a kuma loƙacin saiga mutane biyun nan sun shigo suna zama gefe da gefen gadon. A ladabce na gaidasu suka amsani fuska sake har suna tambayar yadda na kwana. Da lafiya na basu amsa tea me zafi suka ce na sha yanzu jet ɗinmu zai tashi in zanyi tafiya inda ta hawa motace bana iya cin komi hakan yasa nace bana sha, sukace na daure ko kadan ne dai nasha hakan ya sanya sama sama nasha na ture cup ɗin muna fita a bedroom ɗin. Kasancewar babu ƙarfi a jikina hakan ya sanya tafiyane ya koma kamar jan ƙafa nake haka muka kai gaban jet ɗin da ko a mafarki ban taɓa zaton zan taɓa hawansu. Haka jirginmu yayi landing daga farfajiyar gidan muna lulawa tare da keta gajimare...... *SALMAN* A haukace yayi kan surry cikin yanayin fita a hayyaci baiyi duba da halinda take a ciki ba na sumewar da tayi. Cikin zafin zuciya da amsa amon murya ya furta. "I swear u don't die with out tell me what about my bride,nace miki matana take? ko saina yi gutsi² da sassan jikinki kafin ki buɗe baki kimin magana" "Babban kuskure mafi muni a rayuwarka da zakay shine hannunka ya taɓa min ƴa wllh salman" Yaji muryan mom surry ta faɗa daga ta bayansa. Wani irin juyowa yayi a matukar fusace yana watsa mata wani mugun kallo. Itama da nata kallon na kashiga uku ta bishi tana me nufar inda ƴar nata take yashe a some. " wllh wllh taku ɗaya kika fara momi saina sari fuskarki idan kin musu kuma kara ki gani" salman ya faɗi a dake yana saro wata ƴar karamar wuka a jikinsa, Ido momi ta shiga rarrabawa tanasan tijarar salman babu abinda bazai iya aikata mata ba tunda ya rantse domin dama idan ƴan haukan suka motsa masa baya shakkun kowa a gidan bare ita dama daya gama renawa duk kuwa da tana matsayin yayar uwarsa. Wayarsa da yayi ƙara itane ta ceci momi ta fice a sace da zuwan taje ta debo masa police's. Be ankara da ficewar tan ba tunda ya ga daddy'nsa ne me ƙiran. "Salman ina ka shiga ne tun ɗazu ina ƙiran wayarka ba ka ɗagawa? Ka san fa ba na son hakan ka barni a zaune tun dadewa ina dakon jiran zuwanka. "Daddy ka faɗamin dama kitimurmurar da kuka ƙullamin kenan na auramin wannan guntun turawan, shi yasa furr ka hanani zuwa ɗaukar amarya kace yanzu maza basa zuwa ɗaukar amarya? Ehhhhhhh " ya faɗi a matukar harzuke. "Innalillahi, daddy's boy me me me kake nufi ka fahimtar dani, wllh bana ganewa ma ka kulle kaina tell mee tell me maza daddy's boy" "Sauya min matar da kuka yi mana kuka ɗaura min Surayyan momi bilkisu wacce ta gama rabawa turawa jikinta" Zumbur babu shiri Isa manu ya miƙe wani irin gumi na keto masa, "Kai kai banason zancen banza wacce surayyar kuma? Ko so kake saina zundumo maka ashar da cikin wayar ne" "Ba wani fa zancen kare kai daddy kawai kana son raina min hankaline wllh idan baku nemomin duk inda Merrah take ba wllh² saina tada hankalin kowa a gidan" "Kai durun uwaka dan ubanka yo aini a baybai ka kifeni ka fito kamin filla filla yadda zanfi ganewa" ya karashe maganar yana faman safa da marwa shi kadai yasan tashin hankalin da yake ciki idan har da gaske salman din yake. "Allah yasa ba shawuwa kayi da yawa ba" Daddy ya faɗi kayan jikinsa na jikewa da zufa idan har ta tabbata ba'a ɗaurawa salman aure da yarinyar ba ta tabbata kenan wannan shegen yasan shirunsu akan shi kome?. Ya ayyana hakan a zuciyarsa yana jin zuciyarsa na kartar ƙirjinsa da yake jin zafin har a cikin jikinsa. "Kayi shiru kenan da haɗin bakin naka ta tabbata ko daddy" "Haba haba salman kasan dai bazan taɓa ma haka ba saidai inda da wannan munafukar uwar taka suka haɗa baki suka muna fincemu dagani har hakai wllh boy" Daddy yafaɗi "Koma dai miye gani nan zuwa gidan kuma karda ka yarda kowa ya fice a gidan nan wllh domin duk sena kone kowa da kowa na rantse da Allahn da yake busa min numfashi" Yana fadar hakan ga gimtse wayar tare da sunkutar surry ko nauyinta baiji yayi waje, fitar san kofar gidan kuma yayi daidai da loƙacin da motocin police suka faka motarsu mom surry biye a bayansu. "Yawwa yallaɓai gashi nan ma ka gani? Ka gani da idonka ko? Wllh mahaukacine haukarsa ce ta motsa dama sanyi ya fara shigowa ai, karya kashe min ƴata ku kama shi yallaɓai" momi ta fadi tana zaga ye police ɗin. A tsawace police ɗin ya furta.. "Your under arrest her" Wani mugun kallo ya watsama police ɗin yana faɗin. "Akan wanne dalili kenan?" ya fada a rene yana shirin shigar da surry da take a sanƙame cikin motar police biyu sukayi rammm da shi.a fusace ya juwo da niyar naushin fuskar police ɗin ko kafin yayi wani yunƙuri ɗaya daga cikinsu yayi hanzarin buga basa ɗan kulkensa a gwiwowinsa duka biyun, hakan ne ya tilas ta shi kaiwa sukunne yana sakin ƙarar azaba. Amma duk da haka sake ƙoƙarin tashi yake jefa sury a cikin motar yayi yana zaro wuƙarsa yana wani zazzara musu ido. "Na rantse da Allah duk wanda ya sake matsowa inda nake kafin nayi dalilin rasa aikinsa ni saina kassara rayuwarsa kafin nan, kunsan kuwa waye _SALMAN_ ba da iyaka sunan mahaifina kaɗai nake amfani ba nima kaina haɗarine" (Hatsari) wata inkiya wanda alamu ya gama bayyana shine ogansu yama ɗayan dake dab da salman inkiya ta wutsiyar ido. Karaf ya faki idon salman yana komawa ta bayanshi yana damkar hannuwansa wani cikinsu yayi saurin ɗaura masa onka nan suka jefashi bayan motarsu ita kuma mom sury taja motar salman din dake akwai car key nata ajiki. Haka suka wuce da salman ita kuma ta kama hanyar zuwa gidanta, domin ma ba zataje gidansu salman ɗin ba kuma ta rantse wllh ko sama da ƙasa zata hade babu wanda ya isa ya raba wannan auren ya ɗauru kenan har gaban abada, domin farin cikin tilon ƴarta shine fiye da komai data mallaka a duniyar... _MERRAH_ Ba wata tafiya me tsaho bace ta kawo mu garin kano har tsaƙiyar fadar jet ɗin mu ya sauƙe, Nan naga ikon allah yau ga merrah a gidan sarauta (kenan ɗansu suka auramin kome?) na raya a zuciyata ina mai bin bayan su fulani da kuyangai suka kewamu. wata Brai layn car ce da ɗauke mu zuwa ɓangaren Fulani uwargi ga me martaba suraj. Har bakin part ɗinta aka kaimu nan ma kewaye mu akai haka ta kama hannuna cikin nata muna tunkarar katon palon ta bayan passes passes da muka ringa wucewa. A kan wata lallausar kilisa aka zaunar dani cikin ƙanƙanin loƙaci aka cika gabana da kayan ciye² dasu fruit babu kalan da babu, kaɗan naci domin zuwa yanzun sosae jikina ya sake tsanani taurin kai irin nawa da kuma dauriya ya sanya na shanye hakan. Wani lafiyayyen room aka kaini akace nayi wanka na huta hakan kuwa akayi nayi wankane wata farar halp bubu ɗin cotton less aka ajje min tare da blue black ɗin Alkyabba sai su undears haka na shirya bayan shiryawana da kamar 50 minutes aka aiko wata jakadiya wai nazo ana son gani na. Haka na bita domin komi nawa a wannan loƙacin ya tsaya cakkk, kawai ganinan dai kamar wata butum butumi haka nake kallon komi da ido na kuma duk umarnin da aka gindayamin kamar ba merrah ɗin da kuka sani ba. A salin fadar me martaba sarki suraj sunusi shureim fulani tamin jagora, zuciyata in bada bugu babu abinda take min. Kallo ɗaya yamun ya saki murmushi yana faɗin "Masha Allah Fulani yarinyance kuwa ashe na canka daidai" Kaina na sunkuyar kasa dan ba karamin kwarjini yamin ba gaisa shi nayi a ladabce. Amsani yayi yana min ƴar sokana wai shiba surukuwana bane na dena jin kunyarsa. Nidai kaina ƙasa sai wasa da nake da yatsun hannu na. Umarnin tafiya ya bamu fulani ta kama hannuna muka fice bayan adda'ar daya rakani da ita. Suna fita ya sarki suraj ya saƙi wani ƙasaitaccen murmushi a fili yana faɗin. "mabuɗin ƙofofin hasken ta bayyana!" Wayarsa ya ɗauka daga kan tumtum ɗin gabansa. Kai tsaye wata lamba ya dannawa ƙira magana me ɗan tsayi sukayi da wanda yake wayar, bayan ya gama da wanda sukayi kai tsaye lambar da sunan *AK PRINCE* ya bayyan ya dokama ƙira. _KUWAIT_ *AK* Tafiya yakeyi ahankali kamar bazai taka ƙasa ba kaman kuma wanda ke tsoron ƙasan haka yake tafiya. kai tsaye babban sashen sa ya nufa. yana sanye cikin ƙananan kaya black T-shirt da Black jeans tunda yake tafiyar yake wuce dogaraye dake tsaye wanda suka shiga taitaiyinsu suna kuma shiga nutsuwansu,sai ma wani irin girmamawan da suke bashi Ko kallo basa isan shi sai wanda suke take may bayane kawai ke amsa duk wanda ya watso gaisuwarsa ga AK ɗin. A baƙin ƙofan suka tsaya ƙiƙam suna bama kofan tsaro. Ta babban ƙayataccen palonsa ya huce kai tsaye zuwa bedroom nasa, yasa hannunsa kenan da niyar tamfirin wayarsa ya shiga may vebrating dole yaja ya tsaya yana me ɗauka ganin me ƙiran ne ya sanya shi jann ɗan ƙaramin tsuma "mtsssss" kafin ya picking call in tare da manna wayar a kunnen sa. Shiru yayi yaƙi yay magana har saida daga cannn sarki suraj ya furta. "Gaga kana da lafiya?" kai tsaye ya tambayeshi cikin larabci. "Da bana da ay daba jini ba" ya furta yana hararan wayan domin bayason sharuɗan da wannan tsohon yake shimfiɗa masa kai tsaye kamar wani ubansa danya haifi Oummeyn'shi aiba shi ya haifa. "Ka shirya zuwa Nigeria ɗaukan matan dana ɗaura maka aure da ita" "Tunda ga ɗan banza ba mezai hana ka haɗata da matanka su cike huɗu kenan" "ABDOUL-MALEEK wannan ɗin umarni nane" sarki suraj ya faɗi a tsawace yana datse ƙiran... "Mtssssss kama gaji ka sakar musu yarinya uban me zanyi da mata" (Hhhhhhhhhhhh munga ALIEYO ma malam AK😊☺😁 wllh idan kazo kana mana kuka irin na O'o ko hmmmm ubanka zamuci yaseen) Ya faɗi yana me fasa shiga bedroom ɗin domin yana da buƙatar yasha iska. *NIGERIA* _Isa manu pov_ [07/11 9:07 pm] ★~AMMEY LAYLERH🤫: *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 3&4 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ # The Amazing # CHANGER # Destiny # Betray # HotLove # ROMANCE ❤🔥 BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM 💚💛💜❤❤❤📴🔥♥♥ Ahankali yake saƙƙowa daga ƙerarriyar matattakalar benen ƙafafuwan nan nasa fari karr kamar a lashe kai bakace ya taba taka ƙasa bama da kafafuwan nasa, Yayinda lallausan hannunsa me kama da atafa yake riƙe da wayoyinsa guda biyu, ɗaya kirar Samsung ɗayar ƙirar Iphone X Manne a kunnensa yana waya. A nutse ya gama saƙƙowa daga upstairs ɗin yayin da cikin sassarfa yake tafiya amma inka kallesa zakasha a hankali yake tafiyan. Cikin zafin nama se faman harmutsa gashin kansa yake wayan ya janye a kunnensa yana fesar da numfashi. Se faman zuba ƙamshin mayun perfumes ɗinsa masu tsananin tsada yake,yeah shi kansa yasan yana ƙaunar ƙamshi yana kuma kashe ƙudi kwarai a kan turaruka sekace mace. Samm baya ƙashin narka maƙudan kuɗaɗensa akan ƙamshi komi nashi luxury da luxury kawai ake magana. Ba kamar ɗazu ba yanzu wasu shegun hoodie riga da wando rugby guntaye gaba ɗaya black. Fuskansa sanye da black prada goggle saboda kai tsaye baya iya shiga rana bai rufe idanunsa ba. Jikin nan sai walainiyan ɗaukan idanu yake. Tunda ya fito compound na gidan tight security ɗin dake zagaye da harabar wurin suka wani irin kame tare da sara may, mutane biyun suka yi gaba wasu biyun na take musu baya kai tsaye gaban shegen manyan car's ɗin dake jibge wuri guda suka nufa. Wata kafurar Colombia land aka buɗe may ya shiga, wanda kafff masarautar babu me irinta domin iyaka kuɗin ta idan wani me ƙaramar kwakwalwar yaji takan iya juyewa a take tsaban tsadan motan. Arms ne ya shiga driver sit yaja yana me rufewa, manyan motoci sosae suke shirin fita dashi amma ya dakatar da hakan ta hanyar musu nuni dasu zauna baya da buƙata. Kai tsaye motor'n arms ya cilla hancin motar suna nufar git din farko, nan suka shiga ratsa get get na gidan harsukar harabar masarautar, saida tight security'n suka tabbatar da motor'nsu Ak yayi nisa sosae kana suka rufa baya tare da dogarai. Kai tsaye Arms _SHISHA BAR KUWAIT_ ya nufa. land cruiser prado ɗin dake bin bayan motan security'n ce ta faka daga gefen kwalta na shiga Bar ɗin. Zaid dayaga fitan AK ɗin shine ya biyo bayansu, A parking lot na bar ɗin arms ya faka motan ya ɗauki good 10 minutes kafin ya ziro fararen sawayensa zuwa kan tap bries na harabar wurin. Gaba ɗayansa ya fito yana me nufar cikin wurin inda ƙiɗeɗe ke tashi kai tsaye na yaran manyan ƙasan. Wurine keɓantacce daya kasance ba kowa da kowane ke zuwa ba domin wurin kansa ba kowane ya sani ba. Da sauri mahboob dake ƙoƙarin fitowa daga wani passes na daban ya koma da baya, wayansa ya zaro a aljihun wandon jikinsa kai tsaye Mahaifinsa Al-hussien ya dokama kira Ana daga wayan ya furta. "Da da yanzu nazo wuce ta shisha bar naga shigan Ɗaya a cikin biyun su ko AK ko ZAID domin bamuyi kusa ba bare na tantancensu rungume da budurwa" daga tacan banji mene aka ce may ba naga dai ya koma cikin inda ya fito. Ak kuwa ɓangaren daya kasance na musamman ne ya nufa arms da kansa ne ya masa odaring tsadaddun wine, wani farin balarabe da ya shigo ne ya matsa zuwa ga Ak ya fara saving nashi drinks. Ɗan ɓata fuska yayi yana karɓan drink a wine glass da saurayin ke bashi, a nutse ya fara sipping na wine ɗin yana jingina da jikin cought din room ɗin. ɗan rolling idanunsa kafin ya fara tafiya zuwa inda pot na shisha yake sabon pipe dake leda yabuɗe yasa sannan yakai bakinshi ya zuka kafin ya ɗagakai yawani feso hayakin ta hanci da bakinsa cikin wani ɗan iskan salo.... Yana zaune a inda yake har loƙacin kamar walƙiya haka yaga wulgin motocin Da da hussien ɗinsu kuma ya tabbatar ba alkhairi bane ya fito dashi. Da ɗan sauri ya fiddo wayansa "JES maza ki fito da kayan aiki ga wani amaxonties news a bar na gintika layout kuwait" Datse wayan yayi yana sakin wani ɗan iskan smile. Cikin abinda be wuce 50 mint ba saiga almurun motar'n jesra me ƙirar panti grow cruiser land sai Toyota avalon 2024 ɗin dake bayanta. Fitowa tayi cikin shigan baƙar doguwan riga kuwait abaya. Idonta toshe da baƙin shade hannuwanta cikin hand bazan, tayi rolling da vail na abayar sai nose mark ɗin dake faran fuskanta bayan shade ɗin data sanya. "Let's go" ya faɗi ba tare daya bari tayi magana ba da hannu yama gurds ɗin dake biye da ita dasu dakata. Acan ɓangaren su Al-hussein kuma bayan shigansu wajen suka ƙira mahboob ya fito daga maɓoyarsa nan suka shiga neman Ak wuri wuri amma babu shi babu dalilinsa, cirko cirko sukay suna meda kallon kallo tsakanin su alhussein sai wucin ɓacin rai yake fesarwa. "Ban san abinda yasa ma na biye maka ba bayan inada tabbacin har yanzu akwai burbushin allurar haukar data saura a kanka" ya faɗa yana jefa masa wani kallo me kama da irin gargaɗin nan. "Na rantse Da da naga shigowansa wurin nan kuma na tabbata yana a cikin park ɗin nan dole don baici ace yafita a wurin ba" "Kai rufe min baki shasha kafin na ɓarar dakwai kan ka amshin hukuncin dazai biyo baya" Ya faɗi yana juyowa da niyar barin wurin a fusace. Cakkk yaja ƙafa ya tsaya ganin ɗaya a cikin biyun yaran da suke da shegen kamanni na tashin hankali abu ɗaya ne yake banbancesu ta hanyar voice nasu. Sai kuma halayyarsu kai tsaye.... Wani mugun kallo ya jefama jesra dake riƙe da camera a hannunta kafin ya buɗe baƙi cikin hasaluwa sosae ya jefa tambayar... "Waye anan" Wani ɗan murmushi ta saki tana waigawa bayanta tare da furta "ka canka mana kaida ƴaƴanka idan harkai ka gaza ganesu toni taya zan iya ganesun" wani ɗan ƙafta mata ido Zaid yayi ita kuma ta saki murmushi tana juyo da nufin kallon Su Da da. Daidai loƙacin da mahboob ya kawo mata wani zazzafan mari. Baikai ga face nata ba ta baya yaji an damƙi tsintsiyar hannunsa farar fatar hannun yabi da kallo domin yanason tantance ko waye. (Abdoul-maleek) ya furta kai tsaye domin haskensa ba irin me ɗaukar idanun nan bane irin na zaid. Amma idan basa guri ɗaya duk iya lissafinka baka isa tantance da waye kake tare ba sai suna a tare ne hasken ɗaya ke rinjayar ɗaya. "Tabbas wannan wasan lissafi akai akwai maƙirƙiransa" ya faɗi a bayyane yana juyawa ga Ak ɗin baki ɗayansa. Ƙoƙarin cillar da hannun Ak ɗin yayi amma saidai ya gaza amma dake shima tantirin kansa ne gashi soldier hakan yasan ya a karo na biyu hurgar da hannun Ak ɗin. Juyawa ga mahaifinsa yayi tare da furta "Wannan tatsuniyar dole ƙirƙirarta akai don haka ge gida DA'DAH" "Me na tafi kuma na barka kai anan ai kwara kai kaje nina tsaya da sunanka ya ɓaci ƙara nawan ya ɓaci domin kaine sarki na gobe MAHBOOB AL-HUSSEIN EMAAR's" Wani kalan ɗan waro ido zaid da jesra sukai suna me bin ɗan uwan nasu da ido alamar tambaya? Kafaɗa ya ɗaga musu alaman shima me sani ba kafin ya fara taku. Cikin taku ɗaya biyu ana ukun Da'dah ya cafki kafaɗun Ak tare da juyo dashi gaba kallon ido cikin ido suka bi juna dashi kafin Ak ya janye kafaɗansa a nutse yana furfa. "Saidai bana haɗa hanya ko tafiyana da masu rufa ido ko masu face uku sabo da jinina tafashashshene a tafashe yake idan irinsu suna kusanta kansu gareni wannan tafasar da yake zai iya ƙonesu ya saɓule su harma da ƙonewa ƙurmus!" Ya faɗi Yana gin gaba "ka iya buga crikect? Lallai wannan ɗan wasane da yafi ko wanne ɗan wasa kwarewe, da kyau shikenan dai nima ina da wani tsari ni dakai zamu buga ɗan ƙaramin wasa" "Karo da karo shike kayo babbar ɓarna amma in ka shirye muje saidai ka sani kafin buga wasan saika fara tabbatar da ingancin ƙasusuwan bayanka masu zame maka runfa! Dan ABDOUL-MALEEK AL-HASSAN EMAAR's ba kamar alawa bane da ko wanne kare ko doki zai iya lasa bane guguwane neeeeeee!!!" Wani irin shegen fito fifitttt zaid tare da Jesra suka saki a tare. "Hadari malafar duniya funkasau babban girki kaɗangaren bakin tulu a barka ka ɓata ruwa a kasheka ka fasa tulu. Kabewar kan kabari baƙin cikin me taushe murucin kan dutse kake baka fito ba saida ka shirya ABDOUL-MALEEK AL-HASSAN EMAAR's" Zaid ya jero masa duka uban kirarin nan jesra kuma ta shiga tafa masa. A wani irin mugun fusace Al-hussein (Da'dah) yabar wurin domin kwakwalwarsan na gab da gama rikicewa ta juyo idan ta juye kuma hauka ze musu kafin nan kuma dole yana son ganawa da MOH..... "Time is out" Kawai Ak ya faɗi yana barin haraban wurin yana komawa cikin bar ɗin. ★★★ _ALHUSSEN/ MOH_ Wani irin mugun mahaukacin gudu ya sanya akayi dasu hakan yasa cikin ƙanƙanin loƙaci suka isa EMAAR's. A haukace ya fito daga cikin motar duk irin yadda kuyangai da security ke bashi girma da miƙa gaisuwa baya ma ko jinsu duk kuwa da irin yadda yake ƙaunar a bashi girman. So kawai yake ya buɗe ido ya ganshi gaban MOH JIDDOH. Da balin ƙarfi ya daki door handle glass ɗin shiga part ɗin Moh jiddoh, tun daga wawakeken palonta ya shiga ƙiranta cikin sautu me amsa amo faɗi yake "Moh! Moh!! Moh!!!" Mo dake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya gabanta cike da fruit ta watso masa idonunta masu bashi tsoro wani sa'in saidai yau ba hakan a gabansa cikin hayagaga da cira sauti ya shiga furta... "Dole akwai gaskiyar abinda waɗan nan tantiran yaran suka sani MOH! Ki faɗamin gaskiya ki faɗa min gaskiya dole akwai abinda suka sani ko kuma sun gano ba kene _AINIHIN MAHAIFAYAR AL-HASSAN BA_ ko.......... Wani irin shirune ya gitta a wurin na wucin gadi sakamakon wani irin bahagon marin bayan hannun da Moh ta ɗauke fuskar Al-hhussein dashi... "Ban tabbatar da cewa kai cikakken mahaukaci bane sai yau Husseini! Ban san har yanzu allurar mahaukata na kan aikintaba akan kaba sai yau tirrrr dame haihuwar daƙiƙin ɗa irin husseini ! Ka sani wannan ɗin wani shuɗaɗɗan lamarine wanda yake daida da kamar gawar da aka haƙa rami aka bisne, idan kaga hakan ya bayyana wa duniya to kuwa tabbas gawar da aka haƙa rami aka bisne a ciki ƙabarinta ma za tayi magana! Ka sani wannan maganar shekaru 75 ake koshi uban nasu bazai taɓa sanin hakan ba bare zararrun ƴaƴansa haihuwar jiya da giya ta gama illata min rayuwarsu, bare kuma mahaukaciyar kakarsu da kullum take cikin tsananin hauka wacce a haka mutuwarta zata risketa a cikin haukan da ba ranar warkewarsa" "Da gaske nake Moh ke baki gaalamun hakan tattare da yaran ba kuma da kikecewa haka yau shekararki nawa da zuwa dubo _JADDERN ASHAAN_ ɗin. Shima ya faɗi cikin haƙiƙanin gaskiya da gaskiyarsa. Wani marin moh ta sake ɗauke fuskar Da'dah dashi. "Shekaru ubanka nace shekaru ubanka daya mutu zuciyarsa a kumbure, Ka sani _JADDERN ASHAAN_ tana ƙarƙashin kulawanane babu mahaluƙin daya isa zuwa inda take saini koda kuwa aljanine duk hatsabibancinsa duk iya tuggunsa. Matar da take ƙarƙashin ginin merlupin wanda kafff masarautar nan idan aka ɗaukeni sai kuwa ita mahaukaciyar sai mataccen ubanku iyaka mu kaɗaine muka san dashi, ko kai ban yarda na nuna maka sabo da allurar mahaukatanka kan motsawa time to time don haka idon't care your time to be" Fuuuuuuuuuu ta wuce ta barshi a wurin da rikon fuska. Zaune yake yana wani irin fesar da numfashin da yaji yana barazana wa rayuwarsa. Zubar daya gama wankemar jiki na ɗigowa daga saman fuskansa zuwa tafukan hannuwansa da suke a buɗe........ ★★★ ❤❤❤❤❤ _NIGERIA'N_ *KANO* A fusace Sarki suraj sunusu shureim ya shiga ɗakin fulani. Fulani dake kishingiɗe kan Royal chiar idanunta lumshe tana sauraran karatun alqur'ani na _AFIF MUHD TAJ_ ta buɗe idonta tana saukewa akan mijinta. Cikin tsantsan fushi da zallar fusatashin da AK yayi ya furta. "Lallai inason a shirya miƙa _ZAUJATIEY AL-MALEEK zuwa ƙasar mijinta a gobe goben nan! Tunda na fuskanci baya da sauran mutunci da kunya a idonsa harni ze dubi tsabar ido yace nime zai hana na haɗata a cikin nawa matan ta zama cikin ta huɗun! bazai gane babban gatan dana masa ba a yanzun sai zuwa gaba" Wani ƙasaitaccen murmushi fulani ta saki tana gyara zamanta cikin tattakonta ta furta "Ni yanzu miye nawa kaida Abdoul-maleek kuma ai ba'a shiga tsakanin faɗanku, wanda ya shiga kunya yake ji karka damu nima na matsu gaskiyar ta bayyana umarninka abin cikawatane Insha Allah marayme gobe a ƙasar kusa da garin mahaifiyarta zata kwana" Wani kallon kidai iya bakinki ya jefa mata yana fita a room ɗin baki ɗaya kwance ta koma tana maida idonta ta kulle. Kewa da ƙaunar Ƴarta na neman fasa mata ƙirji. So tabbas so take ƴar nata itama ta huta haka nan ta samu cikakken ƴanci ta gaji da ganinta ita ƴan jikokinta kowa daban daban ba a nutse ba so take komai yayi ya gama bayyana kansa. So take ƙaddarar data ratsa tsakani tazo ta gyara tsakanin ramin kura dana damisar haka nan. Gwani wajen iya farauta ya farauci kansa duk kuwa da cewar gwanancewa a yaƙi ba itace nasarar yaƙi ba gaskiyar mutum a kona ina itace nasararsa ita jarinsa. "Sol the promblem very soon Insha Allah" Ta furta tana jin nauyin da kirjinta ya mata na ɗan raguwa kaɗan. Tun a daren ita da kanta tashiga har ɓangaren da Merrah take wasu irin abubuwa ta bata harda na wanka dana turara jiki abubuwadai kala da kala haka ta ringa bata tare ta kwana da merrah ɗin wacce tace ma gobe za'a miƙata ƙasar mijinta. Nidai da ido kawai nake binta domin zuwa yanzu komi ga zama ba daidai ba a gareni daga nan sai nan can yana iya dole zanbi yadda alƙalamin ƙaddarata yake rubutamin daki daki har zuwa matakin da yake son kaini. Washe gari. Tun misalin goman safiyar ranar da yai daidai da talata kwana uku kenan da ɗaura min aure da zuwa yanzun nasan ba salman bane wanda shiba bansan waye mijin nawa ba. Wurin sauran matan sarkin ta rakani muka sake gaggaisawa duk da kuwa cewar mun gaisa dasu washe garin ranar da nazo, daga nan kai tsaye fada aka rakani wurin sarki suraj anan na ɗan jima sosae domin wasu dunkulallun kuramen maganganu daya ringa bani a baybay. Sha ɗaya da rabi na safe duk wanda ya kamata ya fito domin min rakiya ya hallara a compound na fadar. Bisa jagorancin ZAYD SURAJ SUNUSU SHUREIM da kuma jagorancin NAFISA WADA (Fulani) zamu tafi. Haka suka mana rakomu suna me binmu da fatan sauƙa lafiya, Sanyen nake cikin wani shegen almurun golding less. Me shegen tsada wanda kuɗaɗen da suka lasa suke a bayyane. Wata kafurar yellow'n Alkyabba me ratsin fari wacca aka ƙayawatata da brawn ɗin duwatsu ita kanta abar a kallace alkyabbar. ga nose mark ɗin da Fulani ta bani na sanya sai ɓakin glass ɗin dana toshe ido dashi ni kaɗai a raina sai mita nake (Wata sabuwa kenan ko duk wannan ɗin na miye?) Haka na shiya furtawa a raina har xuwa laƙacin da muka kai airpot a cikin wasu mayan ƙerarrun mktoci na musamman , a vip/section muka zauna loƙacin da muka shiga wani irin lumshe idanuna nayi kirjina namin wani irin lugudan da bansan ko na miye ba. Haka jirginmu ya keta hazo muna lulawa sararin samaniya wasu adda'oi na shiga karantawa a zuciyana ko zan samu abinda nake ji na lugudan da akemin a ƙirjina ko zai ragu, "Ya Salam" na furta a bayyane loƙacin da jirginmu ya gama daidaita a sararin samaniya tun ina iya lissafa loƙuta harna koma awanni daga haka har wani bacci yazo yayi awon gaba dani har bansan loƙacin da muka ɗauka ba. Sai idan loƙacin sallah yayi a tasheni nayi na sake komawa ga wani irin kaina da yake sara min kamar ya rabu da jikina. Sha biyun dare muka sauƙa a babban airpot ɗin kasar inda hasken streetling ya haskaka ko ina na harabar airpot ɗin wata dunkulallar farar mota ce tazo ɗaukar mu sai ɗaya kuma data kasance ta security ce. Da taimakon fulani na samu fitowa domin zuwa yanzu kaina kusan zan iyace muku ma a juye yake dan bana gane komi ga komi ɗin da nake gani bibbiyu. Ita ta shigar dani har cikin motar kafin kai tsaye mu lula cikin masarautar EMAAR's. Tafiya bame zurfi bace ta kawomu katon ginin masarautar wanda kallo ɗaya nama ginin kaina ya idasa rikicewa bawai na kyayun ginin ba sai kawai na yadda kaina ya sara da wani irin masifar ƙarfi ƙirjina ya wani irin buga. Take wani mayen zazzafan zzazzabi ya kawo min farmaki. Daidai da loƙacin da muke shiga ginin masarautar daidai wata iriyar Guguwar iska ce na turniƙe sararin samaniya masarautar ta shiga juyamin ilahirin compound ɗin yayi baƙiƙirin tamkar ruwan sama na daf da sauɗa. domin ba sautin da ke tashi sai gunjin fitar iska wanda guguwar ta ke kaɗawa da mugun ƙarfi gami da tashin duk abin da taci karo da shi zuwa sararin samaniya, abin mamaki har da ƙananun duwatsu iskan sama ta ke yi da su tamkar ledoji. ƙara gami da rugugi kawai ke tashi. A Kuma daidai wannan loƙacin MOH JIDDOH ta farka a firgice dafe da ƙirjinta dake barazana wa rayuwarta, wata irin zufa na wanko ilahirin jikinta ba ita kaɗai ba duk wani me alhaki akan haka haka ya tashi a furgicen haɗi da bugawar zuciya data ruhi. Wanj irinhaskene kuma ya gilma shuuuu tamkar ƙiftawar ido. Wani irin ƙasataccen murmushi fulani ta saki cike da nishaɗin ganin yarda al'amura suka soma haske tun a farkon tafiyar. Kallonta ta mayar kan merrah wacce kamar ma bata a cikin nutsuwarta. Gani tayi fatar jikinta yayi wani kalan hasken kyawu gami da jan hankalin duk wanda ya yi arba da arba dasu ga wani irin kwarjinin daya lulluɓe ta nan take. Shafo fuskanta tayi da hannun dama idanunta lumshe sumar idanunta na ɗigar da ruwan hawayen dake bin saman kuncinta. Kirari ta shiga jerama mahalicci tare da ambato a bayyane ta furta. "Ga Haske nan tafe a cikin masarautar EMAAR's me maganin duhu har abada zakara shi kaɗaine sarki. Masu rufaffun ido su farka haka nan game buɗaɗɗen na ainihin nan a gabanku! Makamin yaƙin ga bayyana!" To ai shikenan saimu gimtse haka nan ko?😊😁😀 # Shin me kalaman Waɗannan mutane suke nufi ne kam wai?# _SHIN WACECE JADDERN ASHAAN?_ _SHIN WACCE GASKIYAR BIYUNIN MAHAIFIN SU AK SUKE GUDUN SU AK ƊIN SU SANI?_ _SHIN MIYE HAƊIN MERRAH DA MASARAUTAR EMAAR's ?_ # Shin wanne kalan wasane za'a buga tsakanin AK da kuma Al-hussein (DA'DA)?# Duk ku biyo ni *AMMIEY LAYLERH* don warware muku zare da abawar dake cikin wannan littafi na *MIKIYA* Wanda koda kuɗinka saida rabonka Hajiya idan kin shirya jin kitumurmurar dake cikin wannan littafin saiki biyo *AMMEY LAYLERH* da ɗarinki biyar domin ayi tafiyar manya dake Hajjaju🙅🙌. Kibar tagumi😱 nibance kowa yayi tagumi tsakaninki da Allah idan har kinsan halin ɗari biyar ɗinne baki da to nayi haƙuri ki turim ɗarinki Huɗu nikuwa na antayaki *PAID GROUP* namu da muke posting kullum Insha Allah..... *Idan kin shirya saya saiki min magana a wannan number'n* 08104493215 *Idan kuma kai tsaye account naw kike da buƙatan shima ganan* 3206656358 Maryam Nasiru Fisrt Bank *Sayen na gari maida kuɗi gida koba haka ba😟😵😰 Dob Allah karmu ɓatama juna loƙaci idan baki shirya sayaba karkimin magana, Masu zagina harda ma masu kiran ai ance marubuciyar MIKIYA ta rasu ku sani Allah ne me kashewa da rayawa. Wata ma data tambayeni nace mata paid ne kai tsaye cewa tayi shikenan tama samu* _Kunsan dana tambayeta inda ta samu me tace min? Kai tsaye cemin tai a wurin ƙawarta, ni kuma sai nace mata saidai kuma banma fara rubutun part Two ɗin so dan allah a faɗi alkhairi ko ayi shiru😯_ [07/11 9:07 pm] ★~AMMEY LAYLERH🤫: *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 5&6 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ # The changer game's # Romance scene # His bloved_friend Meerah # His love towards ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ A daidai wannan loƙacin na'urorin dake jone da jikin me martaba sarki Hassan Al-hassan suka ɗauki wani irin kururuwar daya farkar da duk wani makusancin dake jikin ɓangarensa. AK shine mutum na farko daya fara bayyana ta cikin wata shegiyar ɓoyayyar hanyar da ko su Oum basu san da ita ba. Shigansa ɗakin daidai da gilmawar inuwar mutum ɗin da yayi wanda kai tsaye bazai tantance ko mace bane ko namiji. Wurin Paah ɗinsa ya nufa domin dama tunda ya dawo kasar baccin kirki bayayi, kullum yana cikin tsoron mahaifinsa da yake a tsakiyar damisai masu farautarsa. Hankali tashe yayi kan me martaba wanda daidai da shigowar shaƙiƙansa suma hankalin tashe. Kai tsaye hakan ke musu nuni da an sake _poisoning_ Sarki Hassan kenan? "La haula fi sha'atullah!" Shine kawai abinda OUM ta furta wani irin jiri na kwasarta. Da sauri zaid ya tare da tana faɗuwa a jikinsa zuciyarsa na wani irin mugun bugu. "Yau mun shiga Innalillah wa'inna ilaihir raji'un" Moh jiddoh ta faɗi tana yin kan me martaba, Wani mugun kallon da Ak ya watsa mata ne ya sanya ta jan birki jikinta ɗan rawa. RAZEERNERH (MAH) kuwa wani irin rumtse idanu tayi tare da cizar lips ɗinta da ƙasan hakorinta tanajin zuciyarta na mata bala'in bugun da tunda take bata taɓa jin irinsa ba sai akan mutum ɗaya. Kai tsaye Ak yama me martaba ɗaukar jarirai yana barin donpor room ɗin dashi, domin kai tsaye kulawan paah ɗinsa yake son yake son ta dawo hannunsa. "Kai jinin masu ɓakin jini ina zaka kaimin _ƊANA?_ bayan ga dr shazra ajaan nan na zuwa duba shi" "Daga yau na dakatar da duk wani likita dubamin mahaifina, a yanzun kulawansa yana ƙarƙashin iko nane kai tsaye idan kuma dame ja bismillah hanyar a buɗe take right?" Yana faɗar hakan ko inda suke bai sake kalla ba saida yakai hanyar fita kana murya a kausashe ya furta. "Ka biyoni da Habeebty _Ashaan Clinic resoom_ " Kai tsaye zaid daya san dashi yake ya rufa masa baya wannan ba loƙacin tashin hankali bane dan haka sauran jama'ar ɗakin suka rufa musu baya. ★★★ Da wani irin mugun speed yaja motar yana ficewa daga baki ɗaya passes ɗin mahaifinsa. Kai tsaye motar ambulance ɗin Masarautar ce ta ɗauki Oum A harabar building ɗin clinic ɗin Manyan Mercedes Benz black biyu na bayan ambulance ɗin ko kyakkyawan parking basuyiba sukai saurin fitowa Babu Wanda hankalinsa ba'a tashe ba sabo da tsananin tashin hankalin dake cikin zukatansu na ganin yadda AK ya shigada me martaba yayinda jigogin jikinsa suke jin rayuwarsu baya iya kwatanta rayuwa babushi ba, yayinda wasu ɓoyayyun zukatan suke jin Allah yasa nesace tazo kusa Ashshe ta gaida umma bi ma'ana ya mutu kenan. Mutuwar data kasance rigar kowa ko kayi fata ko karka fata dole dole dolen dole dole kasan zaka mutu kuma fa ita mutuwar nan ɗaya ce in akayita ba'a taɓa dawowa har gaban abada abadan, don me kuma zaka ma wanin ka fatan ya mutu. Arikice suka ƙaraso jikin ambulance ɗin da Oum ke ciki daidai loƙacin da nurses na cikin masarautar mata tareda doctors kusan biyar sukayo kan motar aka fito da ita. Cikin gaggawa akayi ciki da ita itama tun a hanya ake ɗaura mata ruwa dama tun acikin ambulance an ɗaura mata cannula tare da fara mata injections. Wani irin yarfar da hannuwansa zaid yayi yana jingina da jikin motan tare da kulle idonsa kansa na wani irin sara masa. Cikin wani irin tashin hankali likitoci da nurses ɗin asibitin suka rufa su Ak baya ganin Me martaba sarkinsu me adalci cikin wannan mummunan yanayin. Bayansu suke bi hankali tashe har zuwa cikin private aminity emergency suka shige, Da hannu yama sauran dactor's nuni da suje waje kafin cikin fusgar magana ya furta musu. "Oummuna! Habeebty itama tana da buƙatarku" Da kanshi ya shiga bama me martaba taimakon gaggawa bayan wasu dogon aune aune daya masa, wata iriyar ajiyar zuciya ya kawo a sadda me martaba ya kawo wani gauron numfashi. Su kuwa waje Wani irin kuka Razeenerh ke rusga tare da sauran mutane tuni wadda basa a wurin ma duk sun bayyana zuwa yanzun kuma. Wani irin rawa Jikin Adeenerh yake ganin yadda jikinta ke rawane ya sanya Jesra matse hannunta cikin nata hannun da ƙarfin daya sanya adeernerh ɗagowa. Jikinta ta faɗa tana me fashewa da wani irin cunkushashshen kukan da tun farko yaƙi zuwar mata... Dr Abaan Areef ne ya ƙaraso harabar inda duk suke tsaye babu wanda ya iya ko zama a cikinsu, kallon Razeenerh yayi sai kuma yaɗan saki ijiyan zuciya tare da faɗin. "Sorry ma'am you will have to wait hia and please calm your self insha Allah he'll be fine we'll do our all best just pray for him! And duk ku daina musu kuka Insha Allah komai Fine" Yana faɗin hakan Ya juya ya shige tareda wasu nurses biyu dasuka zo shigewa da gudu zuwa emagency room ɗin da oum take. Baya jesrah tayi cikin tsananin tashin hankali tareda fashewa da wani sabon kukan ganin yadda likitoci ke gudu suna shiga ɗakin Oum ɗinsu. uzaid dake gefenta ne yayi saurin tarota cikin qarfin hali ya buɗe bakinsa daƙyar shima yasamu iya furta mata. "Please Uktie just pray for him kinji and kiyi ta musu du'a kuka baya taɓa maganin damuwa okay?" Wani sabon kukan ta sake saki tareda rintse ido tana me furta. "Ya Allah ka bama Paah sauƙi tare da oum sauqi da sassaucin wannan masifa! Ya Allah ka zame musu bango majingina a cikin rayuwarsu Rabbi ka hana wani mahaluki damar sake taɓa mana paah ɗinmu! Innalillah Wa'innah ilaihir raji'un wannan ɗin wacce iriyar ƙaddarace Mai wuyar cinyewa..... Saurin rufe mata baki Mah ta yayi da sauri tana kallonta da idanuwanta dasuka kaɗa sukai jajir tsabar tashin hankalin da suke ciki ga wani mugun bugu da wani irin sanyin da taji yana ratsa mata har cikin jikinta. Juyawa tayi ahankali ta kalli gefenta daidai isowar Ak arikice ko gani sosai bayayi tsabar tashin hankali yana isowa ya tsaya cak tare dabin kowa na wurin da jajayen idonsa. Kallo ɗaya zaid yama Ak ya ɗauke kansa wani hawayen da besan sanda suka taruba sun cika jajayen idanuwansa shima nan take yaji gwiwowinsa sun gaza ɗaukarsa ya zube gaban ƙofar roon ɗin dake kusa dashi tareda rufe fuskarsa da tafukan hannayensa hawaye na tsinke masa masu zafi da ciwo... Ɗauke kansa yayi daga kallon zaid ɗin yayi ganin halinda da yashiga zuciyarsa na qara nauyi sosae. Har hawayen da yake ta ƙoƙarin dannewane na neman gangaro masa loƙacinda ya ɗago kansa ya ɗora idanuwansa kansu Mah tare da jesra da suma kukan suke, kallonsa ya mayar kan Adeenerh tana zaune gefen AYESHER tana ƙoƙarin kwantar mata da hankali. Al-hussien kuwa hannuwansa goye da bayansa sai kaiwa da komawa yake ya haɗa wata uban zuba. Moh jiddoh ma tsayen take hankalinta ba a kwance ba domin hankalinta ya rabu kashi biyu ne, neman hanyar da zata sadata da musassin abinda ya farun take, "Me hakan ke nufi?" Ta faɗi da tayi zaton a zuciyarta ne, Mahoob dake dab da itane ya furta. "Me kuwa hakan ke nufi bayan sake poisoning paah da akayi,moh nifa an fara sanja min tunani wllh yanzu zuciyata ta kasa zama wuri guda me waɗan nan jeron gwanon abubuwan suke nufi? Me yasa ake kullum cikin tryn na rayuwar paah ake? Me yasa duk sanda hakan ya faru Oum jesrah ke shiga comma itama?...... Tsawar da mahaifinsa ya buga masane ya sanya shi shanye sauran maganarsa ba tare da ya ida ba. Duk da ƙarancin shekarunta hakan besa ta gane mayucin halin da addarta deenerh take a ciki ba. Tsamm ta miƙe daga jikin mah kuma har yanzun bawai daina zubar hawayen tayi ba Hannuwan Adda deenerh ta riqo cikin nata tare da kwantar da kanta saman sholder na deenerh nan. ɗagowa ta sakeyi A Karo na biyu tana me sake riƙe dukkanin hannuwanta biyu tanata qoqarin ganin ta kwantar Mata da hankali cikin hawaye da tsananin tashin hankali ganin kamar ko bata a hayyacinta ne, Sabo da tunda abin yafaru ko motsin kirki batayiba bare hawaye saidai jajir da idanuwanta sukai Sam ita tafiso taganta tayi kuka yafi sauqi akan wannan halin dataga tashiga, Cikin muryan kuka jesh ta shiga faɗin. "Yi kuka! Kiyi kuka Adda deenerh paah ɗinmu ne fa baya da lafiya tare da oum, kinga duk nan kuka muke muma kalla ki gani! Kinga can gacan ma kalla _GARGALION'n_ ɗin Oum ma kukan yake hawaye yake zubarwa a karo na farko a rayuwasa tunda ya mallaki hankalin kansa..... Wani irin rumtse idk yayi yana barin wurin da sauri zuciyarsa na ƙoƙarin faso ƙirjinsa ta fito dole Anzo gaɓar da bazai sake be wani mahaluƙi damar sake taɓa may mahaifiba, Wasan yazo ƙarshe captering ɗin ya isa haka nan. Lumshe idanuwanta dasukai jajir tayi cikin tsananin tausayin _*Abdoul-maleek*_ Tabbas dukkaninsu suna cikin wani hali Amma shi ya fisu dan kuwa shu ƙunci da Sauyin rayuwa tuni ya daɗe da wargaza komai na cikin duniyarsa, ya tsallake yabar ƙasar sa. Yabar kowa nashi duk dan bama maƙiya ƙafa dan kuma ahalinsa su rayu cikin aminci tunda ta fashimci shi ɗin yafi tsole idanu. _AK_ Ahankali yake jujjuya ƙaramar kwalban dake gabansa wacce ajikinta aka rubuta Carbon Monoxide Poisoning da manyan baƙi, wacce yaci karo da ita a loƙacin da yake dab da barin ɗakin me marta ba. poison ne mafi matuƙar haɗari wanda kuskuren amfani dashi kan iya lalata sassan jikin mutum yayi damage nasa kai tsaye. Carbon monoxide poisoning itace poison ɗin da ayanzu samunta keda matuƙar wahala saboda haɗari da kuma illar da takeyiwa ɗan Adam kai tsaye. Ya tabbar da wannan cctv footage ɗin da yayi setting da na'urorin ɗakin ne ya toni asirin duk wanda yayi ƙoƙarin harar Mahaifin nasa. Murza kwalbar yaci gaba dayi ahankali fuskarsa ɗauke da wani irin ɓacin rai da fusatar da zuciyarsa. Hannunsa ɗaya dake ɗauke da cigarette ya kai bakinsa tare da zuƙan hayaƙin cigarette ɗin ya fesar cike da bacin rai, Kana ya ɗaura ƙafarsa ɗaya akan ɗaya haɗi da maida idanunsa ya lumshe. Wuta ne sosai keci azuciyarsa wutar da har yau ta kasa daina ruruwa. Amma saidai wayanda suka yi yunƙurin ciyar da paah ɗinsa poison ɗin ayanzu wutar ƙiyaayyar dake ci azuciyarsu tafi wanda ke ruruwa acikin tasa zuciyar ya sani, domin suma sun san sunyi kuskure tare da saɓanin lamba tunda harya suka bari ya farka kuwa. Ko so suke su ɓallo ma kansu hasalin haukarsa. Wanda zallar sarauta da isa da kuma uwa uba miskilancinsa suka bisne hakan. Lallai idan har suka bari allurarsu na sojoji ya motsa masa tabbas za'a ɓarin makauniya dole. Insha Allah daga rana me irin ta yau har gaban abada kenan da wani ze sake yunƙurin kashe mai mahaifi ba amma illar da sukeson yi mishi yafi su kasheshi muni ma. Haƙiƙa kowa damar shi yake nema a hannunsa shi kuma ya samu daman, saboda haka zaiyi amfani da loƙacinsa koda hakan na nufin rasa abubuwa nashi da dama, dole bazai ƙara saken da dahar zaa kuma yunƙurin cutar da paah ɗinsa ba ciki kuwa harda rayuwarsa. Hayaƙin cigarette ɗin ya saƙe zuƙa tare da buɗe rinannun idanunsa. "Its time for me to take revenge!!" Ya faɗa yana me miƙewa tsaye tare da juyawa ya fice daga cikin ɗakin. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ _MADINAH_ *emirated place* shine kalmomin da wani babban majigin dake kusurwa kusurwa yake rubutawa yana kuma haska kowanne sashe na ciki place ɗin. Wani babban majigi ne na daban dake rubuce da manyan baƙin *Ash mayesh* Abinda ke rubuce kenan da manyan baƙi masu sheƙi da nuna haske a jikin wani katafaren signboard na karfe mai tsada. Wanda shi kansa signboard ɗin kallo ɗaya zaka masa kasan yaci kuɗi ...    Haɗaɗɗen gini ne irin na masarautun nan da sukayi zarra sukayi fice a cikin manyan masarautu. Yana yin tsarin ginin kuwa tsaf zaka ɗauka hotel ne ma saboda tsananin yadda yake da kyawu, da kuma passes daban daban dake cikin emirated ɗin wasu shegun benayene iyaka ganinka wanda aka tsarasu da iyaka zallar gilashi. Masarautar Madina kenan! Masarautace me cikakken iko wacce take taƙama da Al'adarta da kuma Addininta. Masarautar _Ash mayesh_ ginanniyar masarautace wacce take tsaye da ƙafafunta tun iyaye da kakanni, tun a wajen masarautar zaka fahimci ba ƙaramin Mutum ne ke mulkar Masarautar ta Ash mayesh ba cikin cikakken iko da kuma ginshira haɗi da wani irin kwarjinin daya ma duk wani family daya dangaci Ash mayesh ba. Bare kuma azo kan uwa uba me mulkartar baki ɗaya kaima me karatu ai kasan babu ƙarin bayani domin ɓatama kai loƙacine domin magana ake ta sarkin sarakan masarautun duniya. Wasu Arnayen Colombodia's car's ne shigo masarautar a tsiyace. Duka tarin motocin kalansu ɗayane domin a ka'idar masarautar basa fita da mota masu kaloli na samfurin banbancin company's. Bawai motacin ne babu ba A ahhh suna da tarin motocin na hauka ma kuwa wanda da za'a mutum iyaka wurin adana motocin cikin wannan masarautar me cike da ƙarfin iko kaɗai sai sun ishe har tattaɓa kunnenka rayuwa ba' a cikin talauci. Idan mutum ze fita ka'idar masarautar koda motoci hamsin zaka fita to dukka iri ɗaya zaka ɗauka in colombondia, in Bugatti, in Ralls R Rayce, in mercadex benz, in Toyota avalon, in jeep, in magarland, in Bcc, in Gtv, in Thailand, in colombian, kai duka dai ganan duk kalan da zaka fita dashi to zaka fitane da duka rakiyan wasu shegun tigh securitie's dogarai. A nan mahaukacin street house parking loot kawai na ada motoci suka faka. Tundaga kan sady pary, peery mian kowanne da sunan sa a wajen da motar da zasu faka daga rank ɗin jerin tagwayen sunan wuraren adana car's nasu yake. Mai karatu idan nace zan tsaya zayyano muku adadin kuɗi masu tarin yawa da aka kashe wajen zuba ado a departmen house kawai na adana motocin ma wanj sabon ɓatama kai loƙacinne sabo ma kuwa. Fari kall ɗin matashin da perry mian ɗin suka kewayena ta hanyar masa garkuwa. Matashi ne daya ɗan fara manyanta kaɗan wanda kuma na tabbar zallar hutu da kuma jin daɗine suka ɓoye manyan tan nashi. Cikin wani irin tafiyan ɗaukan hankali ya fara tafiya da zaratan sawayensa, perry mian ɗin nan jere a gaba da bayansa wasun su riƙe da wayoyinsa wasun su riƙe da systerm's nashi wasun su kuma ɗauke da lugage brifcase nashi. Tafiya yakeyi cikin tsananin gajiyawa da kuma cunkushewar da zuciyansa ya may tun ƙarshen wayan sa da ƙanwansan kuwa na safiyar ranan. Da sashen shi yayi niyan nufa amma kuma abinda yay masa tsai a kahon zuciyansa ya hana hakan tabbatuwa, dole ya nufi haromian Ash mayesh entrance na fadar mahaifinsa Sarki _ASHFUDDEERN MAYESH GAANTE's_ Tun daga harabar masarautar ya fara cin katari da manyan kuyangu, bayi, barori, ko wanne da kalan uniformɗinsu komai na masarautar tsare yake. Duka wasu nau'in ma'aaikatan dake compound na wurinne suka tsaya da duk abinda suke kawunansu ƙasa kasantuwar wanzuwar Babban ɗa ga sarki ash mayesh wato _Jalaludden Ash mayesh Gaante's_ Bayason hayaniya ko wacce irice kana bai fiye yawan magana ba shi yasa kwakwkwaran motsi ba'ayi idan yana da wanzuwarsa a wuri, hakan ya sanya ko irin busar algaitar nan baya da buƙata bare kirari. Mutum ne daya kasance me wani irin zafin zuciya wanda ya haddasa tsoronsa a zuciyar kowa. Saidai yana da tsananin tausayi zuciyarsa me raunice akan duk wani abu daya kasance rauninsa. Duk inda ya ratsa na'ura ce aikin buɗe masa hanya da rufewa bayan tayi kuruwar sanar da wanzuwarsa a wurin. Haka harya tsinci kansa a babbar fadar mahaifinsa me ƙarfin iko akan addinin musulincinsa. Wani farin dattijon balarabe ne ke gishin giɗe akan wata lafiyayyar Royal cough me tsananin laushi. Idanunsa sanye da wani yankakken farin gilashi na ƙara ƙarfin gani, jingine yake da cough ɗin Alqurani me girma riƙe a hannunsa gefen wata farar dattijuwa ce zaune hannunta riƙe da bowl ɗin dake ɗauke da yankakkun fruit tana ɗauka da slick tana sanha may a baki. Kansa ya sauƙe kas yana sakin ijiyar zuciya gabansa na mugun buga mai domin tsoron faɗan da yasan dole dolen dole yariskeshi ahar kullum indai zaiyi ido biyu da mahaifan nasa. Bisa bijerewa umarninsu da yayi na ƙin amsar sarautar da yayi shi kima alhalin ba laifinsa bane sun riga da sun sani, Wata shuɗaɗɗiyar ƙaddara ce data gimla ta cikin rayuwarsa shekaru masu dan dama wanda. Amma duk da hakan baya taɓa shallake faɗan Ash da kuma Queen Lajja ɗinsa. Ba tare da Ash mayesh ya duba inda yake ba ya furta. "Uhmmm meke tafe da isashshe kuma a wannan loƙacin?" Idonsa sam ba'a kansa yake ba yana a kan Al'Qur anin da yake dubawa. "Ya Abana DID........ Taryar numfashinsa mahaifin nashi yayi ta hanyar ɗaga masa hannu "Na sani DIDI tayi magana dani kai tsaye kuma nayi magana da zayeed ba buƙatar maimaicin hakan" Da hannun ya masa alama da yajekawai ɗan satar kallon Lajja yayi saidai ko ƙyallin idonta be samu gani ba jiki mace a sanyaye ya juya yana farin barin parlorun. Saida yaje daf da ƙofar fita ya tsinkayi nusassiyar muryantan me cije da zallar damuwa da rauni tana me faɗin. "Lil Anum Asha tazo inason ganin ta" Saurin juyawa yayi yana ɗauke kwallar daya tarun masa da zayeed Ash yakusa cin karo. Saurin taro ɗan uwansa yayi yana faɗin "Subhanallah jalaal Ash lafiyanka?" "Kaje kazo ma da Lajja lil Anum asha" "Asha anum? okay" Sakinsa yayi yana komawa da baya wani ɗan jiriri na shirin kwasar sa ya kayar. Jingina yayi da jikin glash yanajin sadda idanunsa ke cikowa da ruwan hawaye ya rasa ta yadda zaiyi yagaya kawo ƙarshen waɗan nan abubuwan da sukayi jerin gwanan wa rayuwarsa, Yana a yadda yake zayeed ya wuce da Lil Anum asha wacce kallo ɗaya tama Pappin nata ta ɗauke kanta tana me fuskantar gabanta. Fuskansa babu walwala ya bar wurin yana ɗaukar entrance ɗin da zaya sada shi da passes house ɗin ba tare daya nemi abin hawaba. Tafiya me ɗan nisa ne ya sada shi da sassan ginin gidansa me wani irin amintaccen kyawu. On tampring door handle ɗin yayi kana ya kutsa kansa da babban palon magamar gidan baki ɗaya. Oum Anum asha tana zaune hannunta ɗauke da Sultan meerah Jall. Da sallama a bakinsa ya shigo bayan ya cire cover shoe ɗin dake ƙafarsa sanyi da ƙamshin palon na shigarshi loƙaci guda. Da gudu irin nasu na yara nufo inda jalaal ash ɗin yake, ɗaukar yaron yayi yana mannashi da ƙirjinsa da yake buga masa, da hannu ya yafito Oum Asha kyakykyawar macece sosae. Fuskanta ɗauke da murmushinta mekyau ta ƙariso gabansa kwantar da gefen kafaɗarsa tayi tare da furta. "Komai na duniya dan haƙurine komai zai wuce kamar wani abu bai taɓa faruwa ba kaji Zauj" Kanta ya ɗan shafa zuwa fuskanta shima yana faɗin. "Bath first kafin dinner pls" Zare jikinta anashi tayi hanyar sama ta nufa don cika umarninsa. "Amma yau Asha Jikinta yayi sauƙi right?" kanta taɗan kaɗa may tana me ƙarasa hayewa saman, bata ɗauki woni dogon loƙaci ba ta fito tana me sanar ta gama haɗa mishi Sauƙe sultan meerah yayi ya nufi upsaid ɗin.... ★★★ Kowa besan da zuwansu ba har sai washe garin ranar domin kowa yana a cikin alhinine, kuma alhamdullih Oum ma ta farka saidai Ak yaƙi bayyanama kowa hakan me martaba kuwa dama tun a daren ya farka. Jesrah ce tama fulani jagora har zuwa ɗakin da Oum take ba tare da Merrah taje ba domin ita kanta jesrah ɗin bata san fulanin tare take da baƙuwa ba. Ta jima sosae tare da oum ɗin kana ta koma kodan merrah data baro ita kaɗai, shi kuwa zayd suraj yana can tare da zaid Emaar's da kuma arms da dama shima yana a cikin masarautar...... _Bayan kwana_ Alhamdulillah zuwa yanzun oum tana shashinta ta warware dama shock ne har yau babu wanda ya sake ganin me martaba AK ya kasa ya tsare a halin yanzun ma yana part ɗinsa. Kuma babu mahaluƙin da yayi gigin zuwa ko kofar sashen. Sosae fulani tayi jinyar merrah kuma itama oum ɗin bawai ganinta tayi ba tunda itama kusan a kwancen take. Zaune suke su duka A ƙayataccen palon oum ɗin domin yin dinner, Ak da zaid ne kawai babu se merrah da ba kowane yasan da zuwantaba ita dama. Fulani ce ta ɗan dubi jesrah tare da fadin "Kije ɗaki ki tahomin da baƙuwa" Da mamaki ta ɗan dubi kakar nata tare da faɗin "baƙuwa kuma grenny?" "Ehhhhhh zakije ko tsareni da idon zaki tsaya na aiki uwarki tunda ita na isa da ita!" Tsammmm ta miƙe domin tasan halin kakar nasu ba wasa take dasu ba. Babu jimawa kuwa sai gata riƙe da hannun meerah. A sanyaye ta zaune kan kujerar data saura ita kaɗai wacce take fuskantar kujerar da oum take zaune kai tsaye. Gaisar da duka mutanen palon tayi wanda ya sanya oum ta kusan kwarewa da tea ɗin da take sha, wani irin ɗago kanta tayi daidai meerah na sake ɗagowa tana me sake gaisar da oum ɗin ganin kamar ko bata jita bane. Wani irin tarine ya sarƙeta idanunta kafe akan merrah ɗin. Da sauri zaid ya ɓalle gorar ruwa yana bata a baki tare da dan buga bayanta kaɗan, Mahaifiyarta ta kalla tare da faɗin "Mommah wannan ai DID...... Saurim katseta fulanin tayi ta hanyar faɗin "eat itt, yanzu loƙacine na dinner bana magana ba ok?" Duk yadda taso ci gaba dayin dinner ɗin kasawa tayi dole itama fulanin ta miƙe tana me mata magana data bita zuwa ɗakin data sauƙa. Magana sukayi sosae wanda sai faman ɗaga kai oum take tamkar wata kaɗan garuwa, sun jima kafin ta fito tare da kama hannun meerah tana faɗin "Yarinya na muje mu sake gaisawa ki bani labarin ƙasata" Ita dai merrah cike da kunya duk wannan zafin kan ya tafi nashi wuri na wani ɗan loƙaci. Itane tayi ta janta da fira harta samh taɗan sake idan ta mata tambaya daƙyar take bata amsa. Amma kuma mamaki sosae take da ganin matar domin ka tsaye fuskan wancan tantirin na ƙasar Nigeria take a face na matar, saidai tasan gari banban Allah ɗaya domin babu ta yacce za'ai wannan kamilallar matar tama haɗa jini da wancan da satar mutane kawai ya iya, kuma ma tasan me zai kawo wancan babban criminals ɗin cikin ƙasar nan kuma ma har gidan sarauta me girma irin wannan. Sallar zuhr itane ta fito da meerah daga sashen oum. Bisa taimakon jesra da kawai taji merrah ɗin ta shiga ranta kai tsaye ta komar da ita har sashen da fulani take. Itama anan tayi sallar nan suka fada fira bata sake jin ƙaunar meerah ɗin ba sai da taji ashe itama jornalish ce wato ƴar jjarida, Dan duban Fulani tayi fuskanta na bayyana zumiɗinta ta furta "Ayya Mommah dama zaki bar mana merrah anan dan Allah!". Dake babu wanda yasan da batun auren sai Oum da shi kansa Boss ɗin wanda shi harma ya manta da wancan batun na Sarki suraj. "Gata nan dama ai tazo kenan tunda Yayanki take Aure" "Da gaske mommah wanne amma akie zaid aka aura mata ko?" "Abdoul-maleek, dai waye yaje nig a cikinsu?" Wani irin zaro ido waje Jesra tayi tana rufe bakinta da hanunnunta, "Wai kinanufin Gargalion din Oum ne yayi aure ba tare da mun sani?" Wata harara fulani ta watsa mata tana faɗin "Tunda kina matsayin uwar ne meza hana ki raba auren tunda baki sani ba" Daga haka ta miƙe tana bar musu ɗakin domin jirgin gobe zatabi Insha Allah ma kuwa. A ta can ɓangaren Moh jiddoh kuwa Abubuwane suke neman hargitsa mata kwakwalwar kanta, domin Abubuwan da suka faru cikin kwanaki biyun nan zuwa uku. Shin mene fassarar abinda ya faru da ita a daren ranar can? Shin me hakan ke nufi Kenan sanya idon da akama ma hassan Al-hassan ya ninka na baya. Da ita a ranar taso aika shi inda ba'a taɓa dawowa har gaban abada, me wannan nu'urar take nufi kenan wani ya ganta kome? Amma idan tai duna da ganin har yanzu babu wanda ya magantu a kan maganar sai wani sanyi ya ziyarci zuciyarta. Amma har yanzun abunda ya faru ya gaza barin tunaninta domin kamar tarihi na shirin maimaita kansa kenan, rabo da taji irin wannan yanayin tun a sadda da ɓatar da _AYESHERH_ babbar ƴar sarki Hassan Al-hassan ta farko. A ranar da tabar cikin masarautar a ranar akayi makamancin irin wannan yanayin idan lissafint ya tafi daidai kenan yau kimanin shekaru ɗɗaɗɗai har Hamsin da arba'n da shida kenan. A fili ta furta "me yasa tunanin yaƙi barin raina ne?" Haka dai tayi ta tunane abubuwa maban banta na mata kai kawo a tsakar kanta. Zumbir ta miƙe tamkar wacce aka zabura ta firta "JADDERN ASHAAN" Fita tayi a duhun magrib ɗin cikin shigar ɓatta kama kamar yadda ta saba. Wani surƙiƙin yankakken daji ta nufa na wani shashi daga cikin masarautar. Tayi nisa sosae ta tsinkayi muryan mahboob ata bayanta yana faɗin "Kai waye wannan tsaya anan, Ko waye kada ya kuskura yayi ƴunƙurin guduwa domin zan saki Nightingale, da Rhino da pig tare da unicorn su yagalgalamin namansa" Ɓari jikin moh jiddo ya ɗauka cikin tsantsan tashin hankali mara misaltuwa tasan ba shiri take da mahboob ba bare ya fuskanceta,ta kuma san tana gudu zai saki su pig ɗin kamar yadda yayi alƙawari. Cikin dakewa da kuma kame fuska tana dawo da ainihinta na jiddoh ta tsaya cahkkkk. Cikin wani irin shegen tuggu ta taryi numfashinsa tare da faɗin. "Taya zaka saye da haka ita dama kuskuren kunya ai da hauka ake naɗeta, wato fahimta kayi da ina bibiye dakai shine zaka wayance da faɗar haka! Idan baka sakar min suba kaiba haifaffe bane a cikin _ASAAD EMAAR's_ ubanka da yake gudun mahaifarsa dan ubanka da uwarka _SOFIYYERH ANAAN_" A gabanta yaja ga tsaya riƙe da ƙugu kallonta yayi daga sama zuwa ƙasa kana ya fesar da iska yana me faɗin cewa "Ai shi ba lusari bane da zai zauna zaman dogaro dana wasu, neman halak ɗinsa yake kinga kuwa babu laifi da bai zauna zaman jiran tsammanin na wani zuciyarsa a tsaye take shi ƙamm Kuma zaman. _ENGLAND_ yan zun ya fara muje kuma ko yanda babu kowa na ɓalla ƙafafuwanki na zubar anan" "Tirrr da haihuwar ɗa irinka wllh Assad ya haifamin masifa har abada jinin uwarka Sofiyyerh da jinin Maryam ba alkhairi bane a gareni masifa ne ku a cikin rayuwata" Kota kanta baibi ba haka dole don kaucema zargi tabi bayansa suna komawa ta barma gobe. Washe gari jirgin fulani ya lula bayan ta sake duba jikin me martaba da sukayi magana sosae da shi, Anan ta tajama Ak mugun gargaɗi akan matarshi. Shi kallon basu da hankali daga ita har mijin nata ma yake musu yasan kawai gigin tsufane ya fara kamasu. In banda haka Shi me zeyi da wata mace kuma ai ya ɗauka dan jin daɗi da samun nutsuwa ake yin auren?, to shi kuma duk baya da buƙatar hakan wine ɗinsa tafiye masa komai na cikin duniyar idan aka ɗauke mahaifansa. Dan haka ko maganar bebe wani muhimmanci ba yace koma wace idan ta gaji da zama tama ware da ƙafarta, Shida kansa ya kaita airpot zayd suraj nta famar tsokanarsa yana cewa kardai daga baya ya kwarema matarsa kuma yazo yana musu mimison goɗiya wllh ubanshi zasuci, haka jirginsu su fulani ya tashi cike da kewar ƴarta........ A gimtae *BY AMMEY LAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 7&8 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ # The friendship # Romance scene # His bloved_friend Meerah # Meerah Ak drama's ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ _NIGERA'n_ ~Lagos~ Tunda Isa manu yaji abinda ɗan nasa ya faɗa ya tattare nasa ya nasa ya gudu daga gidan baki ɗaya, Idan ya gama haukar tasa inyaso daga baya sun fuskanci juna, Amma kuma saidai me? Washe garin ranar sai labarin yasha banban.domin kuwa kai tsaye gidajen jarudu suka juya labarin kamewar da mom surry tasa aka mai da wani labarin na daban. _A wayewar garin yau kahadi mun tashine da rikicin kame babban ɗan wannan shahararren uban ƴan siyar wato Isa manu, bisa auren manufa da sukaso yi da wannan shahararriya fitacciyar ƴar jaridar wato, _MARYAM ABDULLAHI GWANI_ {MERRAH}. Wanda kai tsaye black mailing mahaifinta yaso yi tunda kowa yasan malam Abdullahi gwani babban malamine. Don dama bayau manyan ƙasarmu suka saba blackmailer's na mutane ba saidai kuma shi Allah ba azzalumin bawansa bane dan haka ma shine ya kuɓutar da merrah daga sharrinsu, ganin basu sami cikon burinsu bane ya sanya babban ɗan nasa yunƙurin kashe ƴar yayarsa da aka misanya masa da ita a matsayin Merrah ɗin..._ Wannan labarin da isa manu ya riska a washe garin ranar shi yafi komai ɗaga masa hankali.domin tuni labarin ya zama shine very latest a safiyar ranar, mantawa yayi da komi yaje har station ɗin hankali tashe domin ganawa da ɗan nasa, sai de amma sammm salman ya hana uban nashi ganinsa. Shi kuwa isa manu babban burinsa kawai so yake yaji daga bakin ubanwa waɗannan maganganun suka fito, domin tsananin tashin hankalin da yake a ciki yafi gaban kwatance. Haka yabar station ɗin hankali tashe kai tsaye babban gidan gonarsa ya wuce domin tattaunawa da ƙashin bayansa masu cin mushe tare masu fuska biyu a cikin al'umma....._ Daga nan kuma suka saki duk wani baɗakalar party'n da su salman suka gudanar tun ana saura kwana biyar bikin. Har dama becholer's night ɗin da sukayi wanda yafi ko wanne haramci tunda buguwane sukayi sosae tare da romance na ƴan matansu. _MOm surry_ (Hajiya Nafisa) Wata kafurar dariya ta kwashe da ita tare da doka ƙafa harda su riƙe ciki a loƙacin da take ganin labaran data tsara kai tsaye ta fiya maƙudan kuɗaɗe domin a fitar da labarin, "Koya yaci tuwa dani! Hhhhhhhhhhh ba kunce ku ƴan iska bane wllh inhar ba zaku risina ba yanzu wasan ya fara. Gashi tun a zagayen farko ni ce winner's idan kun shirya muje zuwa a sannu zanta bankaɗo manyan sirrika ina tonawa Hadiza kiyi haƙuri dolece ta sanyani hakan" Wani murmushin kina kasheni da salonki mom Surry ta jefi mahaifiyarta dashi, hannu ta bata suka kashe tana me cewa. "Farin cikinki a rayuwata shine gaba da komai shalele! Ki rubuta ki ajje salman isa manu har gaban abada naki ne ke kaɗan ki indai ina raye. Ba tare dako kishiya yayi yunƙurin yi miki ba yadda ni kaɗai na rayu da mahaifinki don haka kema ke kaɗai zaki rayu a naki gidan kiyi yadda kikeso da gidan dama me gidan gaba ɗaya" "I sonki mommana!" Surry ta faɗi tana me rungume mahaifiyar nata dan tapping gadon bayanta ta shiga tana furta. "Wannan alƙawarinane Shalelen mommah kar kiji komai" Acan gidansu salman kuwa idan hankalin Mum salman yayi dubu to a tashe yake, ganin ɗan nata a hannun hukuma domin sammm ita bata da masaniya akan auren manufan da mahaifinsa yayi niyar masa da yarinyar kawai dai abinda ta sani tasan bata son aurenshi da ita yarinyar har cikin zuciyarta domin haka kawai taji babu alkhairi a auren. Sosai hankalin Malam Abdullahi ma ya sake tashi, kenan ta tabbata Allah tseratar masa da ƴarsa yayi daya aiko masa da tsohon abokinsa ta hanyar nemawa jijinsa aurenta. Su kuwa sauran matan gidan da haryau sun gaza gano wanda aka ɗaurama meerah ɗin aure dashi sshine yafi komai soya zuciyarsu. Tunda malam Abdullahi'n be faɗa musu ba suma sai bayan ɗaurin Allah ya sheda musu cewar Allag beyi da salman ba amma Alhamdulillah basu tozarta ba domin kai tsaye wani tsohon abokinsa da dama nemarwa jikinsa auren yazo ya tarar da wannan matsalar yace kawai a daura auren a take. Wanda dama Malam Abdullahi'n yana cikin tashin hankaline domin ana dab da ɗaurin auren aka bayyana masa wasu shegun miyagun halayyar salman ɗin, yana cikin alhinin ne kuma Allah ya kawo masa mafita da ɗauki ta hanyar ɗaura mata auren kai tsaye ba tare da fuskantar wani tashin hankali ba. Wannan shine ainihin abinda suka sani kaɗai. Kuma duk iya kissa da kisisinarsu sun gaza gano mijin da aka ɗaurama merrah aure dashi kakaf garin lagos, sun kuma gaza gano wanene tsohon abokinsan daya ambata musu....... Anne kuwa baka isa gane ainihin abinda ke rai da ruhinta ba. Abinda ta sani kawai shine banbancin bugun zuciyarta daya sauya akan yadda take fuskanta akan auren salman, a loƙacin da malam gake me sanar da ita ga ainihin abinda ke faruwa a taje taji bugun zuciyanta yana sanjawa da wani irin sanyi sanyi Me kama duka sassan jiki a hankali. Toshe kunnuwanta tayi ga duk abinda yake shige da fice akan lamarin auren merrah ɗin. Domin taji nutsuwa kam ba ƙarya akan shi wannan auren nata na yanzu akan na baya, hakan yasa ta shiga binta da tarin adda'_oin kariya a duk inda take wannan kenan. Tana tsaye daga tacan bayan ƙofar kitchen take leƙen Mum salman dake zaune ta rafka uban tagumi. "Ai kaɗan ma kuka gani don baku ga komai idan har ban wargaza wannan ahaliba niɗin ba wushiyatu bace" zeey ta faɗi tana me sakin wata shegiyar dariya ƙasa². Kamar wanda aka hankaɗo sai gashi ya faɗo ɗakin babu ko sallama. Da sauri ta miƙe tana taryarshi tare da faɗin, "Aha Ina salman ɗin kuma Alhaji?" "Hmmmmmmm" ya saki wata ajiyar zuciya yana zama tare da zame hulan kanshi yana firfita da ita, "Alhaji magana fa nake ma! So nake ka warware min komi domin ni kaina a kulle yake da wannan batun, kana ina ita surayya'n ko duka aka haɗa aka tafi dasu?" Ta sake jeho masa wata tambayar ganin me tankata ata farkon ba, "Aike zan tambaya tunda kin haɗa baki keda ƴar uwarki kunci amanata,wllh Hadizah kiji tsoron Allah ai dama nasan tunda baki so aurensa da merrah ba dole zaki ɓata!. Saidai banyi zaton da wuri haka ba tunda muma amfaninta kaɗan ne a garemu, daga inda muka gama da ita jefarta zamu a bolar da muka tsinta, Amma shashashan shirmenki ya ɓata komai Hadizah" "Aika sake rufenin ne Alhaji kenan dai ta tabbata auren manufar kuka so yi da ita yarinyar kenan?" Sammm isa manu ma ya gaza bata amsar komi, domin wani irin turiri zuciyarsa ke may ta tabbata dai kenan dole akwai wanda ke bibiye da al'amuransu, Lallai yayi sake da yawa amma ba komi hakan ma tamkar sun zaburar dashi ne. Duk da yadda mum ke masa magana shareta yayi upsaid's nashi ya nufa yana tsane uban zufar dake keto mishi, harta ɗau hanyar saman itama domin bin bayasan sai kuma tayi saurin juyawa tana me nufar bedroom nata car key nata ta ɗauka tare da fita waje, Cikin wata dallekiyar Mwb ta faɗa tun kamin ta isa get take danna hong da ƙarfi don kai tsaye tanason suyi magana da Addarta ne Mom surry. Zeey na ganin fitar mum tayi wuf tana me nufar saman Isa manh. Yana tsaka da wayarsa yaji ƙarar door handle ɗin da aka taɓa saurin janye wayan yayi tare da katsewa ganin zeey ce, wata doguwar ijiyar zuciya ya sauƙe wani munafikin murmushi ta sakar masa tana ƙarasowa inda yake. Hannu ya ware maga a take kuwa ta faɗa jikinsa Hannuwansa ya sanya yana zagayeta tare da tambayarta. "Ta fita ne me gidan?" Ɗan ɓata fuska zeey tayi tare gyada mai kai, kumatunta ya lakata cike da ssheƙiyanci ya furta, "Yau kenan anji tausayina za'a kula dani uhum?" Wata shegiyar hararan gefen ido ta sakimmai a ɓoye daga nan suka shiga sheƙe ayarsu a ɗakin Aurensa na sunnah... _KUWAIT★_ The third season of *Winter Wonderland #EMAAR's* has kicked off, offering a unique winter experience that combines entertainment and fun activities for the entire family. #الكويت *UMAYMAH POV* Zaune takai wani irin zafi take ji yana ratsa ta tun daga tafin ƙafarta har zuwa tsaƙiyar kwanyarta, dalilin hakan nema ya sanya mata karkarwar jiki tamkar wacce ta ji kiɗan gangi. Wanda hakan ne ya haifar mata da gumin da ke ttsatssafo mata a kowacce kafar da ke cikin ilahirin jikinta. Ba yau ne karo na farko da hakan ya taɓa faruwa da ita ba, sai dai a wannan karon ji take tamkar an saka ta a tukunya ana dafa naman jikinta da tafashashshen ruwan zafi ne. Da ɗan ƙarfi ta ɗan ciji ƙasan laɓɓanta tana yarfe hannuwa haɗe da lumshe idanunta da takejin su tamkar a watsa mata barkono a ciki tsabar zafin da suke mata. Amintacciyar hadimarta beenanzer da ke bayanta tana mata fifita cikin ƙwarewa a iya makirci ta sake rusunar da kanta ƙass. "Hutawarki lafiya uwar ɗakina takawarki lafiya uwar magajin sarautar Emaar's zinariyar sarautar Emaar's haskenki bai tsaya iya shi kaɗai ba kin haske lungu da saƙon cikin Masarauta. Ina gwanar wani ga tawa! Kin yi taki kin yi ta kowa garnaƙaƙin dutse kike kowa yay karo da ke shi ka faɗi! Hadari malafar duniya kenan. ki kwantar da min da hankalinki Auren da suka ɗaura masa na bazata hakan ba zai sanja komi ɗin a yadda kika san shiba, kin manta kece uwar maza a wannan masarauta? Kin manta babu me gigin ɗaukar ɗaya daga cikin waɗan nan watsatstsun yaran ya basu sarautar Emaar's. Domin kowa shedane na sanin cewar suɗin ba kowa bane su facen drinker's Humanzer's wanda dattin zina da giya suka gama musu fenti, Ki ɗauki wannan auren ba'a bakin komai ki ɗauke shi a matsayin matacce! shuɗaɗɗe...... Wani irin juyowa ga hadimar tata tayi cikin wani irin zallar fusata ta furta. "Kada in damu fa kike cewa beenanzer? Kinsan kuwa irin tashin hankali da nake ciki duk sanda na buɗi idanuna na kalli waɗan nan shegun yaran? A matsayin ƴaƴan sarki hassan Al-hassan wanda sune magadan sarautar Emaar's ko kin mance sune manyan ƴaƴan maza a masarautar nan? shin baki ganin iyakata da mulki sai dai gani sai hange tunda sune manya akan nawa ƴaƴan? ko baki ga yadda komai ya fara juye min ba? Shi wannan tantiran ya ɗauke uban nashi da ina dab da cikar burina Amma shegiyar tsohuwar ta ɓata min aiki, Kuma sama taka an kuma shammatata ta hanyar ɗaura masa aure wanda shine babbar barana a gareni! Ya kike son nayi? Zuciyata na dab da tsayawa da aiki beenah! A ko wanne hali a ko wanne irin yanayi inason a sake tarwatsa ahalin Maryam inba ta kama da ɓatarwa tamkar shekarun baya da aka ɓatar da ƴar Razeenerh to suma a ɓatar min dasu,yanda ko labarinsu ba za'a sake tayarwa bare na baya su riska tamkar da yadda akama Eesha Emaar's" Cike da wani irin tsoro jesrah taja da baya tana me toshe bakinta da hannuwanta, cike da tashin hankali da tsananin tsoro ta zaro ido da tarin mamaki bata gama dawowa hayyacinta ba taji Mum Mandood na sake faɗin. "Wallahi tallahi billahil azeem zanyi komai dan ganin bayan Maryam da yaranta, zanyi duk abinda ya kama domin in kauda _ABDOUL-MALEEK da kuma zAID_ A matsayin magadan sarautar Emaar's masu jiran gado, dan wlh Allah a wannan karon zan iya kashesu bawai ɓata su a matsayin mashaya da kuma maneman mata ba, domin kuwa wannan rana tana ɗaya daga cikin abinda yasa nayi bore a shekarun baya. Amma sai gashi nayi GUDUN ƘADDARAR wannan rana me kama da irin yau!. kuma sai gashi yanzun alamu na gwada min dukkan wani dagewa da taƙarƙarewata wajen gujewa wannan rana irin haka saidai kamar ma biye take da nawa sawayen ƙafa da ƙafa domin al'amura ne keta faman yimin warwara ya zamanane kamar ina dufka ana min warwara. Loƙacin mutuwar _JADDERN ASHAAN_ yayi ba tare da wannn kwalmaɗaɗɗiyar tsohuwar ta sani a tunaninta ita kaɗaice me basira har wani tinƙaho take da babu wanda yasan ida jaddern ashaan take! Bayan kuma ta haifi ɗa mara amfani lusari Tirr da mutum me irin halin Hussein..... Cikin tsananin kaɗuwa jesrah ta juya da sassarfa tana tafiya da baya baya harta samu tabar sassan Mummy Mandood Iska kawai take fesarwa Sam tama rasa ma wanne irin tunani zatayi,gaba ɗaya kwanyarta ta toshe Shin su waye waɗannan Eesherh da kuma jaddern ashaan? Tambayar da tazo ta mata tsai a zuciya kenan, ko gabanta bata gani babban burinta kawai ta ga Oum ɗinta domin tasan ita tana da amsar duka waɗan nan tambayoyin nata. Karon da taji tayi da mutum ne ya sanyata saurin cin birki, itama a nata ɓangaren da sauri merrah taja nata birkin dafe da goshi. "Wayyo kin fasa min goshi" Ta faɗi tana me duban jesrah ɗin da sukaci karo a hanyar shigarta palon Oum ita zata fito ita kuma zata shiga. Dake ba'a cikin nutsuwanta take bane ya sanya ta furta. "Sorry Habeebty banganine sosae" tana faɗar hakan ta shige palon Oum ɗin.... Oum dake tsaye har yanzun bayan fitan merrah ne tayi saurin duban bakin ƙofan, ganin saɓanin tunaninta ne ya sanya ta faɗin, "Jesrah bakin fita wurin aiki bane kamm?" Kanta take girgiza mata tana kuma nufota ɗan daidaita numfashinta dake seezing tayi tana dannar setin haert nata tare da furta. "Oum Su waye _JADDERN ASHAAN_ da kuma _Eesherh_ ?" Da wanj irin masifar karfi Oum ta juyo tare da riƙo hannuwan jesra ɗin cije da matsanancin tashin hankali ta fuskanceta dakyau tare da faɗin. "A ina kika ji? Waye kuma Jaddeern Ashaan? Easher kuma ƴ.. Ƴar...... Sai kuma ta ƙarasa furta abinda take son faɗin sakamon zuciyarta da taji ya mata wani irin mugun nauyi, tare da hautsuno mata da wasu shuɗaɗɗun al'amura maban banta cikin abinda bai wuce second biyu ba. Zaune takai gefen haɗaɗɗen royal bed nata tare da matse hannun jesrah ɗin cikin nata tana fesar da numfashin daya mata tsai a ƙahon zuciya. "Komai ya kusa bayyana kansa, komai kuma ya kusan zama tarihi Insha Allah kiyi shiru da bakinki Allah yana daga bayan me gaskiya" Haka kaɗai Oum ta faɗim ma jes tace ta fita aikinta Allah ya bada sa'a jiki a sanyaye ta fita ba tare data fashimci komai ɗin da taso ffashimta, amma ba komi insha Allah a matsayinta na ƴar jarida dole sai tasan wani abu daga cikin labarin kafin bayyanar komai ɗin kamar yadda oum ɗinta ta fadin mata...... Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sake a loƙacin data gama tabbarwa da cewa jesrah tabar room ɗin baki ɗaya Goshinta takai ƙasa tare da furta. Ya wadud,Ya zul'arshin makin, Allahu ahad kaci gaba da ƙare wannan bayin naka daga duk wani sharrin me sharri. Ya Rabbis samawati wal'ard karkaci gaba dabe mugyaye damar da zasuci gaba da zalumtar keɓantattun bayinka, Allahu kaine Allah kaine me yadda kaso a duk sadda kaso ɗin kuwa Allah ka mana maganin Azzaluman da burinsu suci zalinmu su zalumcemu Ya ilahi ya mujibud da'awati Allah kare ɗaukakin keɓantattun bayinka wanda basuji ba basu gani ba, Allah ka mana maganin wanda suke ganin sunfi ƙarfinmu Allah ka zarta da ikonko na _KUN FA YAKUN_ akansu ya Allah!!!" Oum takai ƙarshen adda'ar nata tana me fashewa da wani iri kasalallen kuka irin wanda ya daɗe yana cin zuciyar nan. ★★★ _AK_ Gaba ɗaya ɗakin tsit yake daga sautin karatun Afif muhd taj bakajin komai a room ɗin sai iskan dake kaɗawa irin ta farkon daminar nan da kuma ta sanyin AC kawai kakeju. Sai wani irin ƙamshin Air freshsheners da turarukaan wuta masu daɗi da babu jimawa aka gyara may, Ɗakine me girman gaske dake ɗauke da setin royel furnitures masu tsananin kyawun gaske White colour sai ɗan adon milk color daya aka musu. Daga ta nan bakin bed ɗin wani haɗaɗɗen kuwait carpet ne me tsananin laushi da aka shimfiɗa wanda yakai har tsaƙiyar ɗakin, daga gefen window's kuma wata keɓantacciyar kuwait sofa ce Ajiye da ƙaramin fridge. daga gefen mirror kuma wani babban table ne da aka jera littattafan Addini shimili guda gasunan, daga ta gefen gabas akayi wani zagayyen wuri na musamman wanda ke shimefiɗe da wata kalan lallausan praymed me taushin tsiya, sai wasu zagayayyun kuwait decoration's irin masu haskaka room ɗin, sammm ɗakin baya da woni tarkace haka yake simple gwanin birgewa wanda mutum zaiyi normal real life nashi cike da bada cikakkar nutsuwa. Agogon ɗakin ne ya buga ƙarfe 11:31 am na ranar yau Monday daidai bjgawn agogon ɗakin yayi daidai da Mirza handle na ƙofar bathroom ɗin da Ak yayi, Anutse ya fara ɗora santaleliyar ƙafarsa me cike da gargasan gashi baƙi siɗik akan ƙaramin carpet ɗin dake shimfiɗe bakin ƙofar bathroom ɗin. kafin ya Ida fitowa gaba ɗaya ya a nutse ya fara taka sawayensa cike da nutsuwa take ɗakin ya gauraye da ƙamshin shower jal ɗin da yayi wanka dashi. Ahankali ya nufi gaban dressing mirror yana ɗaure da towel navy blue iya ƙugunsa da yama wani irin loko lokon ɗauri, sai wani milk saman wuyansa yana goge ruwan jikinsa dake yarara lafiyayyar tsayayyen jijinsa me jini a jika sai faman walainiya take tamkar woni beby sabuwan haihuwa. Wannan fuskar da cikar kamala mai nuna barazana wa maƙiyinsa dole ne ya yarda yaci wannan suna na jarumi kuma ingarman namiji me ji tashen samartaka wanta jinin mulki ya gama ginashi, zuciyar nan nasa samm babu daɗi baƙar zuciya ta ɗan motsa da dukkan alamu kenan yau don a matuƙar haɗe take. Ba kuma komai ne ya fusatar dashi ba sai zancen matar shi da Oum ta masa a daren jiy!, wani ɗan numfashi ya sauƙe a karo na farko tare da ware lumsassun idanunsa yana me sauƙe ganinsa saman Abubuwansa da yake da tabbacin Zaid ne ya kawo mishi. Komai yake yi cikin tacin zuciya yake tsafff ya gama shirya kansa cikin wasu haɗaɗɗun egyptanian riga da wando ya sanya sky blue, pcarp nashi ya zira inda farar lafayayyar cutie face nashi ta ƙara fidda ainihin taswirar kyawu da kuma zatinsa. A natse ya isa gaban Iphone nashi inda sautin karatun ke fita take karatun kuma ya tsaya sakamakon shigowan ƙira ɗan lumshe Ido yayi ya kuma sake buɗewa ya kalli agogon dake manne jikin bango, red lips nashi ya ɗan ciza bada yawa ba yana ɗaukan phone in dama yasan ƙiran bazai wuce Oum nashi bace, ba tare daya ɗauka wayan ba ya nufi hanyan fita, kamar yadda yana yinsa na rashin fara'a yake haka yafito daga cikin ɗakin hannunsa riƙe da key nashi na Keken da yake son hawansa yau. Drectly Sassanta ya fara nufa tana zaune akan wata royal sofa ruwan zuma, tayi crossing ƙafafunta wanda da duk alamu a wurintane Ak namu yayi gado aha. A nutse ya shigo cikin nutsuwarsa da deep voice ɗin nan tasa ya furta "Assalamu Alaikum!" "Wa'alaikas salam habeebty" Zama yayi daga gefen ƙafafunta yana me ɗora kansa saman ƙafafunta cike da cunkushewar zuciya ya furta, "Barka da safiya Oummuna" Gashin kansa ta ɗan shafa kasancewar ya zame pcarp ɗin, kafin a tausashe ta amsa shi cike da kulawa. Apple ya ɗauka daga jerin fruit ɗin dake shaƙe a gabanta. Babu jimawa saiga zaid shima wata harara ya cillama Ak ɗin yana ɗauke kai daga kallonsa, shima yi yayi tamkar be ganshi ba ya zauna aka fara break ɗin dashi. Shigowan jesrah kenan ko zama bata samu ikon yiba oum ta furta, "Maza je kizo min da zauj Al-maleek!" Rassssss gabansa ya bada sautin bugu yana tsayawa daga shan coffee ɗin da yake a tsime, babu jimawa sai gata ta dawo zama tayi gefe da Ak tana faɗin. "Oum bacci ta koma mebi ta gaji ne kinsan yau ita kaɗaine tayi duka dinner ɗin nan" kai kawai ta ta ɗaga mata suna ci gaba dacin kayan karinsu.Ak kuwa wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe yana ci gaba da shan coffee ɗin da ya masa daɗi sosai, bayan da suka kammala yin dinner ɗin jesra ta fita cikin sauriri domin yau ta kusa yin late nema. Zaid ne ya ɗan dubi oum a shogoɓe yana karyar da wuyansa gefe cikin ɗan tura baki kaɗan ya furta "Oum ni yaushe zaki min auren ne tunda kimma biyuna?" Wata daƙuwa oum tama zaid ɗin tare da ranƙwashin kansa da samm baya saka hula ko wacce iri, sake tura bakin gaba yayi yana me sake faɗin. "Kinga dama gobe birthday na don haka saiki shirya min suprise mata a maimakon kyautan da zaki min really?" Yana faɗin haka ya kwasa da ɗan gudu gudun kada yanzu kuma yasha dundu, saman lafiyayyan gadonsa ya faɗa tare da ciro wayansa yana buɗe datan wayan domin tunawa duk wani clips nasu cewar gobene fa birthday nashi.......... To ai shikenan saimu gimtse anan kawai Sai munzo taya murnan birthday koda kuwa a gayyar soɗi ne aha koba haka ba my FAN'S??? *BY AMMEYLAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 9&10 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ You Are My Dream Come True _Meerah AK 😊🙃🥰😍_** Kai tsaye status yayi da, _My people tomorrow is my birthday my celebration comin at 8:10 pm O'clock Wow my people have a crucial celebration at moment time,Happy and axcited to u all_ Kamar ƙiftawar ido da bismillah sai gashi mutane har sun fara replying nashi. Mutum na farko daya fara turo masa saƙo shine Afif taj babban abokinsa da _Happy birthday to my incredible dud in life, On this special day, I want to take a moment to appreciate the unbreakable bond we share. From childhood memories to adult adventures, we've been through it all together. I am so grateful for the laughter, the tears, the late-night conversations, and the unconditional support. You are more than just a brother - you are my best friend, my confidant, and my guiding light. As we celebrate another year of ur life, I wish for you to have Joy that overflows from your heart ,Success that surpasses your wildest dreams, Love that surrounds you always, Health that keeps you strong and vibrantHappiness that fills every moment. May this new chapter bring you closer to your goals, your passions, and your heart's desires. May you continue to grow, learn, and evolve into the amazing person you're meant to be. I am honored to be your ZAID EMAAR's partner in crime, and your forever friend. Here's to many more years of making memories, creating new experiences, and exploring life together. With all my love, appreciation, and well wishes, happy birthday once again dud 🎉_ Daga nan sakonnin mutane suke bude masa suna shigowa kai tsaye na taya shi murnar birthday nashi. Duddubawa ya shiga yi wasu ya amsa wasu kuma ya share ya ɗan 6ata loƙaci sosai akan wayan daga ƙarshe dai sai kashe duka wayoyinsa yayi. Yay bacci abinsa merai da lafiya. Bangaren Ak bayan kammala dinner nashi wani kai tsaya ya ɗauki luzury blue Kekensa yabar entrance na masarautan ma baki ɗaya. Ta wata boyayyar hanya yabi gudun kada waɗan nan natattun suce zasu bishi, Saidai ashe yayi na banza ne domin loƙacin da yake dab da fita wani soldier ya ganshi. A take ya ƙira wasu suka mara may baya amma bata yanda zai gane ba. Daga cann ƙasan ranshi yake jin wani irin boyayyen farin cikin da besan ko daga ina yake ba, Yawo kawai abinsa yake akan shimfiɗeɗiyar kwaltan. Kai tsaye wani Haɗaɗɗen estate ya nufa a anguwar _MASHATLE SHUWAIK_ Estate ne wanda yayi fice yayi shura a birnin ƙasar nasu, anguwace ta manyan mutane kebantattu daga cikin tsiraran mutane ne ke rayuwa a cikin estate ɗin. A wani haɗaɗɗe tsararren dogon gini ya yatsa on tampring na duka finger's nashi biyar door glasses ɗin yayi. Saida suka tabbar da ya shige lafiya kana suka bayyana a gaban wurin suna zagaye ilahirin ginin don wanzar da tsaron lafiyansa. Da kekensa yaci gaba da tafiya a titin gidan da ya wani irin bala'in haɗuwa kamar ba gobe. Ya ilahi wani irin tsararren gidane me ɗauke da ground floor, private entrance , big private garden , 4 bedrooms , big lobby, big maid room, kitchen, 3 bathrooms, private 2 shaded car parking, no landlord lives in the house. Komai na gidan a nutse a kuma tsare haka yake. A wata ƙofar mashiga ya dakata wacce gaba ɗayanta ta kasance ting tihgt ce, sai ruwa da hadarin dubai tsaruwan wurin ya bada wata sassanyar nusassiyar iskane ke kaɗiwa a hankali wanda kai tsaye take tafiya da ƙamshin flower's ɗin da suka ma gidan dama estate ɗin ƙawanya. Nan ɗin ma dai on tampring nashi door handle in yayi. Da ƙafa yayi tafiya me ɗan zurfi kasancewar yau baya da buƙatan hawa lifp. Ci gaba yayi da tafiya da ƙafafunsa haka harya iska wani shegen ploor me azabar kyau da tsaruwan daya kusan tafiya da tunani. A wani entarnce door ya tsaya Akun da aka sanya domin be mutum umarnin shiga ne ta naɗi sautin amon murayansa kana ta bashi daman shiga, Ƙofar wata kuwait dooor flop dark room ce ta bayyana daga ƙasan kuwa farat ɗaya idan ka kalla kai tsaye zakace ruwane ya tare hanyar ga wanda be sani ba. Amma kai tsaye ga wanda ga sani kallo ɗaya zaima wurin ya gane cewan Opp water's tiles ne Malale a hanyan. {Lol😊😂☺ banda ƙauyenci su O'oh ahammmm Munje..... Ta maƙalƙaleni tana ihu da kururuwan waiya ruwa² itafa wllh ba zata shiga ruwa ba😎😎😎😎😫 dan haka masu tsoro close your Ido uhummmmm} Sanyin da yaji ya ratsa har tsakar tafin ƙafarsa ne ya sanya shi ɗan rumtse ido yana ɗan bata fuska tare da cizar ƙasan lips nashi ba da yawa ba, Sai kuma ya buɗe a hanzarce tuna ko a ina yake da wani irin sassarfa ya isa xuwa ga asalin bedroom ɗin domin ba ɗan ƙaramin missing nata yayi ba duk da kuwa cewar rana ɗaɗɗaice baya kallonta ta cikin cct fotage ɗin daya settinlyng da komai nashi. Harda ɗan guntun gudunsa ya isa ka dattijuwar dake zaune ta juya bayanta da dukkan alamu woni abu me muhimmanci take ko take dubawa. Ta baya ya ɗan yi hugging nata yana ɗora kansa akan bayanta. Alqur'anin da take karantawa ta ajje bayan kamar good 5mints da shigowansa, gashin kansa ta shafa yana me sauƙe wata boyayyar ijiyar zuciya. Jin ta taba shine ya bashi tabbacin takai kejin da take son kaiwa ɗinne domin kuwa tun a farkon shigowansa yaga tana karatun alqur'anin. "I miss u so much haskena!" Ak ya faɗi cikin wata kalon muryan da yau kaɗai ya bayyana raunina muraran. " and miss u shalelen Hasken haske!" Kamilallar voice nata ya bugi kunnuwansa, Ɗan lumshe idanunsa yai yana me jin zallar farin cikin ganinta cikin ƙoshin lafiya. "Ya yanayin jikin haskena yake?" Ya jefa mata wannan tambayar kai tsaye, "komai yana ta sake zama kamar a tarihi ne shalele, iyaka kulawanka kaɗai kan wanzar da samun cikakkar lafiyana hasken haske sai dai muce alhamdulillah, tun a nan zaka gane lafiya ba kamar baya ba da nake kan ganiyar hauk........ Kasa ƙarasawa tayi domin ta hanyar toshe mata bakin da yayi, domin a duniya ya tsani jin wannan kalmar daga wurin koma waye bare kuma daga bakinta. "O'ohh kina son zuciyan shalelenki ta buga ne kawai ko J..... Hasken shalele? Pls ki manta komai kamar komai ɗin bai taba faruwaba! Yanzun baga kinan ba darai da kuma lafiyankiba and ya kamata ki goge duka sauran memorie's ɗin daya saura a cikin brain naki hasken shalele right?" Sake shafan gashin kansa tayi tana jan kaɗan ba da yawa ba. "Alhandulillah Allah alhamdullilah I don't have enough words to thank u or described how am feeling right now after open my eyes and see me in front of the apple of my eyes the favourite part of me"Ak yasake furtawa yana juyowa yayi facing matar yana sakar mata wani lafiyayyen murmushinsa daba kowa ke samun kalansaba. Wani irin hawaye ne ya ziraro daga idanunta sanda taji yasake rungume ta sunfi 1mnt a haka sannan yayi breaking hug ɗin yana kama hannayenta yayi kissing nasu. Chaliey robbot ɗin dake kula da duk wani al'amura na gidan Ak ya ƙira cikin abinda bai gaza 3minst ba sai ga wani saƙagon robbot ya bayyana . wanda shi da kansa ya ƙirƙiri abinsa domin kulawa da lafiyan grennpa nashi domin bai yarda da kowa a fannin kula masa da hasken saba. Gidane ke6antacce da babu wani halitta da yasan yana da tun a loƙacin da ya kawota gidan. Komai dake wakana a gidan waɗan nan robbot ɗin sune ke aiwatarwa domin gudun kada aci amanarsa, ko'a ha'inceshi hatta da komai da komai sune suke kama daga kan kitchen har zuwa su moping, wanke² dadai sauransu. Da nu'urar jikinsa yayi amfani ya duba abinda yake son ya duba ɗin kana ya sallami chaliey. Babu jimawa saiga rakatun maganan Yesh,tare da zurat sun cika palon, "Ohh god!" Ya faɗi yana me zamewa ya kwanta don yasan halin yesh ba barinsa zaiyi ba shike nan, "Barka da xuwa babban aboki!"Robbot yesh ya faɗi . "Dud!" Ak ya ambaci sunan robbot ɗin yana me cewa. "Pls bansan stress ka barni kona maka filla² Ka tashi a aiki na ƙirƙiri Afuuh, kai ka tashi a aiki okoy?" Yanajin hakan tun be ƙarasa ba ya ɗauki hanyar barin bedroom ɗin yana daf da fita yace "Battery na yayi sanyi, kana plash nawa yana gaf da samun matsala ayi gaggawar sauyasu tare da charging piont na samu rauni ba dayawa ba kamar yadda nake d....... "Najiiiiii" Ak ya faɗi yana cewa "bani zanyi aikin ba chaliey zai chajeka!" ita kuwa dama zurat tuni tabar wurin. Daga nan baccin daya kwana biyu baiyi irinsaba yayi wuff dashi, Ido sosae dattijuwar ta zuba masa tare dajin wani mugun tausayinsa, "Kana ganin jarabawa yaro sannu ɗan baiwa" Cikin wani irin slow ya juyo da face nashi suwa kan fuskanta, sauƙo da idanuwansa kan fuskarta yayi kallon ta yake kamar ba gobe a hankali ya motsa bakinsa wanda nima da banji meya faɗa ba? wani guntun smiles ta saki tana me sake gyara mishi Konciyarshi, nan baccin gasken yazo yayi awon dashi. _Almost 2:37pm ★★★ A nutsensa ciki wannan yanayin na kamewa da muskilanci yake saƙƙowa a saman stairs ɗin, Sanye yake da 3q jeans black sae armless brown. Hangota yayi zaune cikin babban falon nata hannunta riƙe da mug tana sanye cikin wata doguwar rigar kuwait Jallabiya. Zana yayi a kusanta yana amsar mug ɗin tare da ɗan sipping shayin kaɗan bada yawa ba. "Kafito kenan?" ta faɗi tana kallonsa da kai ya amsa mata domin yana tashi yaji zuciyansa tamay nauyi, Zama kaɗan ya ƙara ya mata sallama ya fice bacin sun tattauna wasu muhimman sirrika. ★★★ _MOH JIDDOH_ "Haba jidd0h Ae tun asali ma laifinki ne da kika bari har ma ya kai tsawon wannan loƙacin muna sponsoring nasa da kinyi duk mai yiwuwa tun a baya kin sa an kawar dashi ne ae yanzu gashinan ya zame mana ƙarfen ƙafa shida shegun ƴaƴan san nan!. Yaufa kimanin 7 days kenan ko ikon ganinsa bamu da bare mu kawo ƙarshen wasan kowa ma ya huta!" "Bazaka gane ba Hussein na fika jin raɗaɗin hakan dahar na raini ɗan kishiyata a matsayin nawa ɗan! Sai yanzun nima nake sake tabbar dacewa ba ɗan ƙaramin ganganci nayi ba! Amma ba komi anzo ga6ar da dole su kwalba su bayyana domin kawo ƙarshen komai a yanxu bana da buƙatar sake jin komai ko ganin komai fa ce lalacewar family'n _JADDER'N ASHAAN_ Ina son kafin numfashinta na ƙarshe bayar ganganr jikinta ta ɗanɗani ɗaci da kuma azabar da hakan shine zaiyi sanadiyar bugawan zuciyarta. domin kuwa tana ji tana gani ɗan data haifa zaice ba itace uwarsa ba tare da shegun jikokinta. Ina buƙatar yau naje tare dakai domin kuwa shine na ƙarshe kuma ta fito kenan, A gaban idonta za'a harbe kan ɗanta bata ikon hanawa Hhhhhhhhhhhhhhhh.......... Ta sheƙe da wata kafurar dariya tana ƙarasa shigewa bedroom nata. ******** _NIGERIA'N_ *Lagos* ****************** _Mariya Kamaal_ Tana tsaye a kitchen sanye take da top irin wannan wanda daga ƙasansu ake ɗinkewa hakan yasa gefen cikinta yake a buɗe sai crazy 4½, shigowanta kenan kanta a kunce a nutse tasa hannu ta tattare shi ta sakashi cikin trap band Yunwa take ji sosae hakan ne ya sanyata dafa couscous jallop bata jima kuwa ta fito ajiyewa tayi a dinning Area tayi sama domin ɗaukar chocolate nata na gado batakai ga hawan stairs ɗinba aka danna bell. ''haiiii waye kuma yake ƙoƙarin shiga haƙƙin ni da kuma babynmu?" da yanayi na gajiya ta faɗa da kuma yunwar da take azalzalarta tana me yarfe hunnuwa jan ƙofar tayi da ɗan ƙarfi Tana sake ambatar, koma dai waye zai shiga hakkin babynmu wlh" "Baban babyn ya dawo domin sammm ya gaza samun nutsuwar zama ba tare daya sake jin dumin babyn da kuma maman babyn ba" Kamaal ya faɗi yana jawota zuwa cikin jikinsa. Ɗan bakinta ta tura sai kuma ta furta "yunwa mukeji first" "Aha go ahead muje na kula da maman baby kar yunwa ta kama min baby tun a ciki" Ɗan rufe idonta tayi alamarn kunya sai kuma tayi saurin janye jikinta tana wucewa gaba, "Ina kuma kike shirin zuwa haka?" ya tambayeta ganin tana ƙoƙarin hawa sama. "Zan ɗauko chocolate nawa ne fa!" "Dawo a nan wai ban hana shan zaƙin nan haka nan ba ne kammm?" Kwa6e fuskanta tayi kwalla na tarun mata "kuma fa kasan idan har bada chocolate naci ko miye ba ba zama yake mun a ciki ba zanyi aman sane Aiyn" "Mrs Aiyn dawo nace badai chocolate bane ganan wani nazo miki dashi" Ya faɗi yana tashi ya dawo da ita yana zaunar da ita kan ƙafafunsa... Shida kansa ya bata abincin duk lauma bayan laum saiya haɗa mata da wannan chocolate ɗin don haka shine wanzuwar zaman lafiyansu su duka tunda ta sami cikin nan kuwa. "Sannu da zuwa Aiyn" Ta furta bayan ta gama ƙoshi abinta tukunna. "Uyummmm saida kika gama cika ciki kana kika tuna damin sannun really?" "To ai zuwa loƙacin ko kallon gabana banyi sosae ne aiyn" Ɗan shafa gefen fuskanta yayi yana faɗin "Babyn Aiyn rigima" Haka dai suka shashance abinsu aikin dabai koma ba kenan. ★★★ Ta buɗe baki kenan da niyar sake wata maganar, amma maganar da maƙale a bakinta sakamakon tozali da idanuwanta suka mata da merrah. Wani irin tsuma tare da yankar zuciya ta tsinci kanta a ciki da kallon meerah ɗin, jinin jikinta kuwa a take ya shigawani irin hautsina mata wanda hakan kai tsaye ke tabbatar mata da tafasa jinin jikinta yake. Ido Oum ta kafe Mah dasu domin ganin reaction nata, Sammm ta gaza janye idanunta akan meerah ɗin da ƙyar ta samu ta fusgo kalmar "Easherh? DIDINA!!!" Da sauri itama merrah ɗin ta juyo da kanta zuwa inda tajiyo irin muryan Anne'nta masoyiyarta sakk. Itama chakkk ɗin ta tsaya tana kafe matar da ido babu wata tantama zata iya rantsewa wannan fuskan Anne'ntane wllh. Saidai ita wannan ɗin tsantsan hutu da jin dadi daya gama huda fatar jikinta da kuma tsananin hasken fatar ta. To amma wannan kamannin ai sunyi yawa kuma dai tasan Anne'nta bata da alaƙa da matar dake tsaye a gabanta. Domin kuwa tasan basa da alaƙar gari ɗaya ma bare kuma ta jini. Hannuwanta suna rawa ta matso ga Merrah ɗin tare da shafan fuskanta cikin wani irin raunin murya ta furta. "Irin kamar ki ɗaya da DIDINA! saidai a yanzu duk inda take nasan tafi haka zama ta iya haifar yake" Hannunta tasa tana kifewa saman na matar da ganinta ya bugar mata zuciya, wllh zata iya rantsewa da'@ Nig taga matar nan babu abinda zai hanata kamata tace itane mahaifiyar Anne'nta duk da kuwa cewan wannan matar baici ace ta haifi ya Annenta ba. Muryanta yana rawa itama ta furta "Da'a ce a ƙasarmu na ganki babu abinda zai hanani cewa kene mahaifiyan Anne'ta" Saurin rungumeta Merrah Mah tayi tana furta "Allahu ahad!! Allahu ahaad!!! Wllh irin muryan Queen Lajja na ce dake" Kamar daga sama taji Mah taji muryan Oum tana faɗin. "Taya barewa zatai gudu ɗanta kuma yayi rarrafe ita ɗin JININKICE! Ƴar gidan Easher'nkice RAZEERNERH" Da wani irin bala'in ƙarfi ta sake rumgume Merrah ƙa ƙam a jikinta tana fashewa da wani mugun kukan daya kusan sarƙe numfashinta. "A ina? A ina MARYAM? Kar dai kice min itane MATAR ABDOUL-MAKEEK? Inkuwa hakane lallai Allah da girma yake kuma shine buwayi gagara misali shi yasa tun a ranan data sanwo ƙafanta cikin wannan gida bugun zuciyana ya sanja, Sanyin da nakeji a tare da Easherh na wllh shi naji tun a ranar" Sai kuma tayi shiru tana ɗan ɗago fuskan merrah idonta bai sauƙa akan komi ba sai kan wani ɗigo da yake kan gefen wuyan merrah ɗin wanda yake tamkar zanen tatto. Sake rungumeta tayi sai kuma sukayi luuuuuuu sakamon sumewar da Mah ɗin tayi. Merrah kuwa dama bata san mike faruwa ba ita dai tasan mafarkine kawai take wanda a cikin mafarkin jinta da ganinta suka jima da shuɗewa, shi yasa ma loƙacin da sukayi bayan itama tabi ta kawai a tunanin ta duk a cikin mafarkin ne Kafin takai ƙasa Oum tayi saurin tararsu itada Jesrah da shigiwarta kenan room ɗin Ak din don ganin Pa'pa'nta. Dawowarta daga wurin aiki kenan don Zaid ne ya isheta akan tayi maza ta dawi zata may wasu abubuwa kafin wannan kayan fushi da bacin ran ya dawo gidan wato AK. Tana zaune bata san sadda ta miƙe tsaye ba zumbir tana furta "Wacce Easher'n ?" Ta tambayi hadimar nata wanda dama shigowarta kenan ta dawo daga fitar da tayi tun da sanyin safiya. dog year rigace a jikinta abaya wacce aka narka manyan kuɗaɗe kafin a siyeta ,saikuma gyalenta data yane kanta sai jakarta da kuma takalminta suma duka designer ne. Damƙar wuyanta tayi tana me sake faɗin"Nace miki wacce Easher'n?,ba tambayarki nake bane wai?" Ta faɗa cikin ɗaga murya wanda hakan saida ya razana Hadimar daganin yanda yanayin Moh jiddon ya sanja loƙaci ɗaya. "Umm ummm dama dama..... "Ummm dama me ki buɗe baki kimin magana dama me? Ta faɗa tana sauƙe wani irin wahalallen numfashi mai nauyi haɗe da dunƙule hannunta A lokacin inka ganta zaka kasa gane inda yanayinta yake,shin baƙin ciki take ji kokuma tsoro da fargaba Ko tashin hankali ne? "Ke beenanxeer wai ko kunnuwanki sun daina aiki yadda ya kamata ne na dawo miki dasu daidai.?" Haka Moh Jiddoh ta sake rikirkita beenah cikin rawan jiki da dama yawanci a kawoma wani gulman wani kake cin ubanka jikinta baki ɗaya bari yake ta buɗi baki cikin sarƙewar numfashi ta furta. "Wllh da gaske ne nazo wucewa ta cikin balcony ɗin Oum jesrah naji tana zance da dukkan alamu ma waya take yine, shine fa na lafe naji tana cewa ƴargidan Mah data batace ta bayyana amma anan ɗin ba ita bace ƴartane ma wacce aka ɗaurama Boss Aure da ita wai Merrah!" Wani irin wulgar da beena ɗin moh tayi duk kuwa da cewar jikin tsufa gareta amma kai dama kallo ɗaya zaka mata kasan cewa irin tsofin najadun nan ne maƙirai. Wata sakakkar ijiyar zuciya ta sauƙe tana jin duniyar ma baki ɗaya na juya mata, kanta kuma na neman juyewa zuwa na masu ta6in hankali. Wayanta dake gefen Royal chiar ta ɗauka tana dannawa da alama wani ko wata take nema a wayar cikin gaggawa. "Hello Hussein? Maza ka bincikamin yanzu shin da gaskene matar da aka aurama Aboul-maleek aure da ita ƴar Easherh ta bayyana kokuma watace ne daban?, ina son bayanai yanzu yanzu sannan ka tabbatar babu wanda ya zargeka don nasan halin haukarka idan ya motsa kana iya kwa6emin aiki" "To shikenan Moh yanzu kuwa zan bincika ɗin" "Idan har ya tabbata haka ne to da akwai gagarumar matsala! don shirin da mukayi tsawon shekaru gaba ɗaya wargajewa zayyi,dan haka ka taka tsantsan ka ganomin komai, Amma ta wata hanyar da sauƙi domin idan harya tabbata Yarinyan itace, kuma ita aka aurama wannan shegen kaga kenan babu Aure tsakanin su, tunda da uwar yarinyar dashi tantirin uba ɗaya suke." Daga tacen Hussein ɗin yaja ijiyar zuciya hankalinsa na ɗan dawowa jikinsa sai kuma ya furta. "Wai to garin ya haka ta faru a bazata taya ma zakice haka duk shirin da mukayi na 6atar da Ita a duniya saida ta dawo? mtswwww aikin banza nikam ba samm ban yarda ba wllh moh" "Karka yarda dan mataccen ubanka! Nace karka yarda hussein a kana kallon yadda abubuwan dai suke kwa6e mana a cikin ƙaramin loƙutan nan" Kitttttt ta datse kiran tana wani irin runtse ido tareda jijjiga kai Kai tsaye Center table ɗin tsakiyar ɗakin ta fasa raga raga tana kuma tsaye, zuciyarta na neman faso ƙirjinta tabbas ta yarda sai yanzun abubuwan da suka faru a wancen ranar komai ya dawo mata a kuma ranar ne ita yarinyan ai tazo, kana a kuma ranan tayi poisoning na me martaba. "Wllh bazan yarda komai ya kwa6e min da wuri haka ba! Meyasa za'ayimin haka? duk Uban tsawon waɗannan shekarun dana ɗauka kenan a banza wllh bazan ta6a yarda nayi faɗuwar baƙar tasaba dole ki mutu yau _Jaddern Ashaan_ Duk kece sanadiyar komai kene kika shigo cikin rayuwata kika 6atamin ita wllh na tsaneki Na tsaneki Keda zuriyarki tsanar daban ta6a ma kowa ba a duniya" Tana faɗin hakan ta miƙe ko kallon gabanta batayi babban burinta kawai taganta a gaban jaddern Ashaan ɗin. Taku take me kama da sassarfa idonta har bata gani sosae zuciyarta kamar zata faso ƙirjinta ta fito. Haka ta ringa shiga tana fita ta cikin wasu 6oyayyan hanyoyi wanda haka har saida takai kanta ga wani surƙuƙun bakin ɗaki me tsananin duhu sosae. Wanda dattin ƙura da yana baki ɗaya suka baibaye ɗakin, da hannuwanta tayi amfani wajen fara share gefe da gefen tsakiyar ɗakin, take wani wuri da aka masa alamar zEr0 ya bayyana. Numbobine tsoffi irin na da ɗin nan suka bayyana a jikin wannan wurin bayan ta danna wata jar alama, numbobin da suka daɗe da zama haddattu akanta ta shiga daddanawa, a take tsakar tilen moples ɗin yaja gefe da gefe saiga wani da ɗaɗɗen gini ya bayyana kai tsaye ta shige ginin cikin ƙarƙashin ƙasar. Wata azabar shi kansa ginin wani ginin ne a cikinsa haka ba tare da tsoro ko fargabar komai ba ya faɗa dakin ƙarshen. Bin bayanta yake cike da fargaba mai cunkushe da tsoro,ita kuma ko waigowa bayanta bata yi kawai tafiya ta ke cikin sassarfa ta ban mamaki wanda hakan yasa dole Mahboob fara haɗawa da sauri-sauri gudu-gudu dan ya cin mata amma ina sai ƙara sauri ta ke harta shige cikin wani surƙiƙin dogon gini. Kai tsaye cikin dogon ginin ta shige shima ya mara mata baya cikin sauri, yana shiga yaga ƙofa ta samu da kanta ta rufe gidan kai tsaye nan ta ke wani uban duhu ya mamaye gidan baki ɗaya tamkar wata yayi nisa, Nan take hankalinsa yayi mugun tashi domin ko tafin hannunsa bai iya gani tsabar duhun cikin duhun ɗakin. Kai tsaye inda Jaddern Ashaan take a ɗaɗɗaure ta nufa wani irin yankawa gabanta yayi ya faɗi zuciyarta na barazana wa gangar jikinta ta hanyar fasar kirjinta ta fito. Cikin wani mugun tashin hankali da ƙinƙinar da bata san tana da ita ba sai yau ta shiga faɗin. "Me me me za zan ga gani hah ha ka ni Hauwa'u?, komai ya gama ƙare min ɗin kenan dai ko kuwa yaya ya?, to kadai mutuwa tayi ta bushe ta zama wannan burbuɗin kasan?" Ta faɗi tana me wawurar kasan da ta ɗan turu wuri ɗaya. Wata walƙiya taga ta gitta idanunta da wani irin hasken daya kashe mata idanunta sai kuma taji kamar an buga mata wani, Sai kawai ta tafi luuuuuu tayi ƙasa a sumeeee........ To masha Allah ai shikenan saimu gimtse anan ba? Hhhhhhhhhhhh Kai wllh nama rasa ta inda zan fara da tamboyinku da kuma yawan sharshinku mutanena. Kawai dai muje zuwa game rabo za'a warware komai dashi. *AMMEY LAYLERH taku ce* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 11&12 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ You Are My Dream Come True _Meerah AK 😊🙃🥰😍_** _MADINAH_ A ɗan tsorace Ash ya janye wayar a kunnensa wanda har hakan ya sanya queen Lajja dake basa gyaran kumba dago da kanta tana me dubansa a nutse. "Lafiya Ashfuddern?" Queen lajja ta tambayi mijin nata, kansa ya ɗan jujjuya mata yana faɗin. "Kamar dai kunnuwa sun ɗan sami raunin jine wllh Lajja, amma kar6a muga ji abinda ake faɗa! Daga lambar Lele Razeerh ne" Itama jikinta na ɗan rawa ta amsa tana manna woyar da kunnenta tare da jin furucin da Oum ta sake maimaita mata itama. "Kunnenka be samu raunin jiba Rahul hakane abinda kaji kuma daidaine" Tsaye ya miƙe har jikinsa na ɗan rawa kaɗan bada yawa ba, "Bani phone na" Ya faɗi a hanzarce. Bashi tayi kai tsaye number'n Zayeet Ash kai tsaye yayi calking. "Ina buƙatar jet yanzu yanzu maza xuwa Kuwait Zayeet Ash!" "Ko lafiya kuwa Abana?" "Ba tambaya nace kamin ba aikin zakamin kona nemi woninka yamin?" "Afwan Ya abana yanzu kuwa an gama" Daga haka ya yanke wayan yana cewa lajja ta shirya yanzUn zasu tafi babu jirah. A take Zayeet Ash yayi magana da pilot ɗin dake driver'n nasu duk inda suke so yayi akan ya shirya tashi yanzu zuwa kuwait. Babu 6ata loƙaci kuwa ya nemi izinin tashi 7 na magrib ɗin, 7:30 jirginsu ya tashi daga madina zuwa kuwait, tafiyan bame tsaho bace cannnn hakan yasa 8:50 suka sauƙa a masarautar kuwait. Kai tsaye Mah dake a sume suka fara gani tun a daren wacce har yanzun bata farfaɗo ba. Ganin me girma sarki Ash a sallar asba ba ƙaramin kaɗa hantar cikin hussien yayi ba, amma sammm hakan be nuna ba ko'a fuskan shi saima gaisawa da sukai cikin mutan taka da tattako. Daga nan masauƙi suka sake komawa ita kuwa dama lajja tare ta kwana da yarinyanta. Wacce sai a sanyin asubar nan ta farka da wasu surutai wanda ba masu ma'ana ba, Da kan lajja take a sake mata alluran bacci domin kwakwalwanta ya sake samun relax yanda ta kamata. ★★★ Ak tun a daren ranan oum ta sanar dashi abinda ya faru wand har kawo kwanan yau be ta6a ganin matar nashi ba, kasancewar sa6ani suke samu kuma ko zaid Merreh bata taba haɗuwa dashi ba. Hakan kuwa yama Oum daɗi domin kakaf labarin abubuwan da suka ringa faruwa tsakanin AK da MEERAH saida fulani ta bata labari wanda hakan shine abinda gafi rinjayar hankalin me marta, ganin duk faɗin duniyar babu mahaluƙin daya taba fira dashi bare batun bayyana kansa wa al'umma, amma ta sanadiyarta ya magantu tun daga nan me marta yasa aka ringa bibiyar masa duk wani motsin Ak ɗin tare da Merrah. Bama iyaka labari kawai ake bashi ba daga karshe komai ake may video nasu har kuwa ranan data kusan faɗawa ƙasar benen nan, anan maganganun yarinyar da kamu kamanninta suka haska may wani muhimmin sirri da tarun abubuwan mamaki, tun daga nan ya fara neman duk wata hanya da zata sada shi da iyayen yarinyar. Saidai kuma kash a loƙacin daya bayyana sai yayi rashin sa'a don saura kwana uku bikinta ma a loƙacin, Harya fara shirin juyawa wani ƙaddarern lamari ya sake haskaka hasken daya fara kalla tattare da yarinyan Harkuwa hakan ya kaishi ga nasarar haɗa aurenta dana mara jin jikinsa. Wannan kaɗan kenan daga cikin abinda fulani ta yankama Oum ɗin. Ak kuwa cewa yayi yau zaiga ƙarshen fitsarar koma wace tada yarda harta amsa sunan matsayin matarsa. Hakan ya sanya kai tsaye ya nufi Sashen mahaifiyarsa duk da kuwa yasan cewarn babu kowa bangaren nata. Kai tsaye daga yasan bedroom na jesrah nan ɗin ya nufa. Fitowanta a wanka kenan domin tashinta kenan alluran bacci itama oum tasa aka mata,sai yanxun take farkawa hakan yasa tana tashi ta fara da wanka don tana son jinta Fresh off kafin ta zauna nazartan komai tunda kuwa xuw yanzun tasan ba mafarki bane ba kuma cikin gushewar hankali take ba. Rigar wankane sanye a jikinta blue colour iyaka cinyanta sai farin towel data naɗe kanta a ciki. Wani mini kuma riƙe a hannunta tana tsane ruwan dake ɗiga daga fuskanta zuwa jikinta. Fararen santala santalan cinyoyinta tar dasu kamar wacce ake wankesu kullum da madara da zuma sai wani colour'n glowing suke. Sammm ita ba ma'abociyan son irin waɗan nan ƙananun kayan bace amma kuma tunda tazo ƙasar dole bata da za6in daya wuce hakan tunda bata isa ɗaura zani ta shiga wonka ba, yoma ina yake babu dama zani ɗayane kakaf kayan kuma tunda jesra daga dashi take amfani idan zatai wanka ta hanata sanyawa amma taƙi. Haka tanaji tana kallo ta ɗauke mata duka zanin harma da rigan akan hakan kuwa har ƙaranta takai wurin oum Amma ta bata haƙuri tace taci gaba da amfani da showel ɗin da kuma bathrobe dele haka take dannewa tayi amfanin dasu ba don taso ba. Towel ɗin dake ɗaure saman kanta ta ware tana kaɗa kanta tare dayin hajijiya domin idan ba jesra bace a room ɗin bata wani amfani da na'urar busar da gashin kai, tafi gane ta naɗo abinta a showel kana ta karkaɗe abinta ta taje shi tas. Sake baza gashin kan tayi tare da ɗagowa haɗi da ɗan turo baki gaba haɗi da faɗin "Jes kin gama dan....... Maganan tane ya maƙale a maƙoshinta haɗi da wani irin zaro manyan idonta masu kalan madara da kuma na ƴan mayen nan. "Ya rabbi.! Ɗan dabar can dai anan?" Harshen meerah da zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri ya suɓuce wajen faɗa batare data shirya hakan ba. Aida wani irin tsalle ta buga sai gata tsaƙiyar bed tare da toshe kunnuwanta da hannayenta tana kurma uban wani ihu. "Na shiga uku Ni! Maryam, Innalillahi yanzu kai nan ɗin ma saida ka biyoni ko tsoron Allah bakaji?. Ka sani yanzun ni killatacciya na haramta da duk wata haɗawa dakai A yanxun haka ina amsa sunan matar Aur........ "Keeeeeeeeeee!!!" Ya daka mata wata kafurar tsawar data sanyata ƙamewa, "Ke mahaukaciyan inace hala? Kinyi ƙanƙanta dana bibiyi tatsitsiyar yarinya irinki nevermine har gaban abada" Duk da cewar a tsorace take kuma kanta a rufe yake da duka tafukan hannuwanta amma hakan be hanata murguɗa masa baki ba tare da furta. "To nidai ko miye na haɗaka da girman Allah ka fice a gidan nan baki ɗaya kaga nan gidan sarautane ba kamar nigeria bane daka saba dabanci wllh idan Mijina ya ganka zai iya halakaka! Tunda naji kowa na gidan tsoron shi yake ance ɗan zafin kaine wllh tsaf zaisa bindiga ya harb...... "Keeeeeeeeee!" Ya sake sakar mata wata tsawar yan faɗin "Allah ya kiyashe na harbe wani saboda mace macen ma ke irinki marar aji" "Wllh zanyi maka ihun ɗan iska tunda ba zaka fita ata arziƙi ba" "Uhumm Aha bara to na matso yadda zakifiyin me dalili ihun da kuma lasisi ganin dai da gaske gadan gadan nufo tan yake ya sanyata miƙewa a guje tayi hanyar data fito wata bathroom. Taku ɗaya tayi ana biyun taji ya ɗamki tsintsiyar hannunta, "wayyo Allah na wayyo Oum kina ina kizo wani ya shigo har cikin gida zai keta min haddi!" Wani mugun bugu ya kaima bakinta a take gefen lips nata yaɗan fashe ba da yawa ba kaɗan, "Idan kuma nine mijin sai kiyi yaya kuma?" Tuf ta tofar da miyau wanda jini ya ɗan biyo kaɗan "Allah ya rufa asiri ma ɗan daba irinki yazama mijina, kasani nan ɗin gidan mutumcine da masu mutumci kuma ka sakarmin jiki domin jikina me darajane me tsadane ba kowanne datti da ƙazamin jiki ne ke haɗa nasa da nawa ba na bayama ban yafe ba wllh" "Sai kuma Akayi katari _ABDOUL-MALEEK HASSAN EMAAR's nine nan a matsayin mijin naki! Idan har baki haɗiyi zuciya a daren yau kin mutu ba ke ɗin baki cika babbar mara kunya ba kuma naki _ZAFIN KAN_ kaɗan bame yawa bane" "Allah ya rufa asiri wllh dana zauna da ɗan ta'adda marar kishin ƙasar sa kalanka kara na haɗiya zuciyan na mutu tirrrrrr da mugun fata" Tana faɗin haka ta yanka masa cizon da yazo may a bazata wanda hakan shine ya bata daman guduwa tana Mirza ma bathroom ɗin Key. Numfashi ta shiga sauƙewa a hankali tanajin yadda zuciyanta ke bugawa, "Mugu! Azzalumi!!" Ta faɗi tana durƙushewa a wurin wani abu me zafi da narka Zuciya na dunƙule mata wuri guda. Cikin muryan kukan taci gaba da faɗin "What do you want?,why did you bring me here?, leave me I can't Meerah yanzu ni ba merrah ɗin da ka sani bace ada ni matan wani ce sunan matar aure nake amsawa azzalumi ɗan daba me satar mutane I hate you." Ashe ma bata sani ba ita kaɗai take abinta don tuni yabar bangaren ma baki ɗaya. Da kyar ta iya fitowa a bathroom ɗin tana jin yadda zuciyanta yake a cinkushe, Sallah ta gabatar anan idda take bacci me nauyi yayi awon gaba da ita duk wainar da ake toyawa kuwa bata sani ba har zuwa washe garin ranar. Da misalin biyu da rabi na rana baki ɗaya duk wanda yake da kusanci da waccen maganar sun gama kammala a babban palon Mah, Harda Sarki Hassan Al-hassan kasancewar jikinsa da sauƙi sosae taron zayeet ash ya buɗe musu da adda'a kafin Sarki Hassan ya furta, "Alhamdulillah Ahar kullum Allah shine abinda godiya me bayarwa da kar6ewa a sa'ilin da yaso!, Ayau ma shine ya sake haskaka mana wani hasken da muka jima da rasashi ta hanyar disashewar daya mana ya bace mana battt! Amma kuma cikin ikonsa da buyawarsa da kuɗirarsa ya bayyana hasken da muka jima da fidda rai da wannan Hasken kwasan kuma da yaso a rana guda, a wuni guda ya haskaka mana shi kansa asalin wannan hasken wato ya bayyana mana ƴarmu da muka jima da cire tsammani daga gareta wato Eash....... "Be kuwa bayyana muku ba wllh" Suka jiyo muryan moh jiddoh tamkar wacce aka wullo daga sama. "Idan har ina numfashi hakan bame yiyuwa bane! Kuma idan harda gaske ne yarinyar itace wacce aka ɗaurama aure da wannan tantirin kenan babu Aure a tsakaninsu kenan?, tunda uwarta yayar Abdoul-maleek ce" "Ba yayarsa bace" Nusassiyar muryan Sarki ash ya daki duka kunnuwansu tare da ratsa tsakiyar ƙirjin kowa. Gaba ɗaya kallo ya koma kansa ciki kuwa harta ita ƴar tijarar wacce dakyar mahboob ya samu ya cetota daga wannan shegen ginin ƙasar. "Kwarai kuwa ba yayarsa bace hasalima basa da wata alaƙa saita musulinci!" Cikin muryan nan da yake fita da kaushi kaushi da kuma hargagi ta furta "To saika mana ƙarin bayani tunda daduk kan alamu daga sama ta faɗo ba haifarta akai ba" Moh jiddoh ta faɗi tana wani harare hararenta. "_EASHERH ASH MAYESH_ , Ita ɗin cikakkiyar ƴata ce ta sunna kuma ƴar Auta ta" "Rainin hankali taya ƴar da na ni ce mutum ta farko na fara amsarta da hannuwana Loƙacin da Razeenerh ta haifeta yanxu kuma don son cika wani mugun nufi kace ba ƴarta bace?, to wllh inma auren kuke son halastawa to kuwa tabbas haramtaccene" "Moh Easherh kwarai ba ƴar dana haifa bace ƴar Ash ce" Wani mugun kallo ta data cillama Hassan ne ya sanya shi shanye maganarsa. "Uhummm tell me ina jiran ka sanar dani ta yadda aka haihu a ragaya" "Ganin a waccen loƙacin MATATA RAZEENERH bata haihu ba har shekaru biyar da aurenmu ne ya sanya sarki ash ƙirana ya sanar danj cewar, Idan har queen lajja ta haihu mahaifiya ga Razeenerh kenen ya bamu duk abinda ta haifa halak malak. amma karna sabarwa ma kowa tun kuma daga loƙacin Zeenerh ta koma can madina da zama da nufin tana laulayi me zafine moh idan baki manta ba a loƙacin haka na sanar dake?" Ya faɗi yana kallar moh ɗin kanta ta gyaɗa mishi alaman ehhhhh ta tuna da hakan, ci gaba yayi da faɗin. "Bata tashi dawowa ba sai a daren ranar da queen lajja ta haifi Autarta mace wacce suma haihuwar taso musu a bazata. A kuma daren naje nazo da zeenerh sai tayi kamar a masarautar ta haihu sai mukayi amfani da hakan gashi kuma dama babyn kamanninta ɗaya da Razeenerh kasancewar uwa ɗaya uba ɗaya ba ƙarya ba. a haka tayi rainon babynta saidai tarin wani abin mamakin sammm babyn taki amsan mama a wurin Razeenerh dole muka renata da madara har takai yaye ba tare da kowa ya fuskanci komai ba. A haka har takai shekaru takwas kwasam kuwa dare ɗaya rana ɗaya sama ƙasa muka Nemi Easherh muka rasa, wanda wannan shine tushen komai har bayan wasu shekaru tun muna san ran wata rana zamu ganta har muka haƙura muka fawwalama Allah komai. A haka mukaci gaba da zaman mu ba tare da zeenerh tayi ko 6atan wata bane, ganin hakan ya santa cemin nayi wani auren ko allah zai bani haihuwar, haka har auri Yasmine wato mahaifiyar Adeenerh abin mamaki ko wata biyu bata cika ba ciki ya bayyana a wurinta wanda kuma wata ƙudirar na allah saiga itama Razeenerh'nan da nata cikin. Kusan loƙaci ɗaya suka haihu fikonsu kwana biyar a tsakani, A kuma ranar da zeenerh ta haifi ɗanta namiji a kuma ranar Yasmine ta rasu. Bayan ta faɗamin wasu maganganu masu girma da nauyi. Rasuwanta babu daɗewa sarkin kano na nigeria ya bani auren ƴarsa wacce ada naso bijerama hakan saida zeenerh ta tunasar dani kana na amince,cikin ikon Allah kallon farko nama maryam naji soyayyarta tsantsa a zuciyana. Ashe Allah ya soni da rahamarsane da naso bijire masa ashe itace cikon mahaɗin garkuwan haskena. Bikinmu babu dadewa sai gata da ciki wacce ansha gwagwarmaya ba laifi baga Moh ba ba kuma ga matar biyunina ba matar hussein kenan domin kiri² suka nutsa tsanarta a fili babu ko kara. Daga inda ta haifi ƴan biyun ƴaƴanta duka maza wata _ABDOUL-MALEEK_ da kuma _ZAID_ Daga nan mabuɗin wasan ya soma har kawo kwanan yau kuwa!!!" A fusace ta miƙe tana furta "lallai na yarda gyaɗa mayaudariyace tunda akayita da kwanso amma ba komai ko anan A-Hassanu ka nuna min ban isa dakai ba na haifekane ban haifi halinka ba" Fuuuuuuuuuuu ta fice tana barin ɗakin domin wasan ai bezo karshe ba dole saita cika burinta kota kuwa shine ƙarshen numfashinta. Daga nan suka sake tattaunawa a tsakaninsu maganganu masu sarƙaƙiya kana daga nan xuwa gobe insha Allah zasu wuce nigiria don ganin cikon miradinsu su duka wato _ANNENMU_ kenan. Da da meerah za'a tafi amma Oum tace su barta suje saisu zo da annen, dake ma har yanzu babu wanda yasan da maganar ko jalal Ash be sani ba so suke sai komai ya kammala kana su bayyanama duniya. Drecly da sarkin kano sukayi maganar kuma dama acan zasu fara sauƙa. 7:50am jirginsu ya lula nigeria kwarya kwaryar liyafa aka haɗa masu a fadar kano kasancewar yau babban sarkine a kasarmu wato sarkin madina da kansa ba aike ba, ƙara kwana sukayi sai a washe garin ranar agains suka sake bin jirgi zuwa lagos kai tsaye kuma sarkin kano yayi magana da Malam Abdullahi gwani tun a daren jiyan. Da misalin sha ɗaya da rabi jirginsu yayi dirar Mikiya a garin lagos nan ma a gidan gwamnan lagos suka sauƙa wasu shegun manyan motoci kusan guda talatin aka shirya wanda duk na rakiyan me girma Ash Mayesh ɗin MADINA ne. A wani irin tsare aka shiryama fitan motocin kansu iri guda ne kasancewar duk wanda yake da labarin sarautar madina yasan cewar basa fita a mabanbanta motoci ko kuwa sunkai ɗari ne ko. Gaba ɗaya motocin Rolls R Rayce ne bugun 2024/2025 Blue black masu ting glass ga wani irin ƙawatan da aka ma motocin da ado irin na zaratan manyan sarakuna, Ko wacce bayan mota tana ɗauke da tambarin _ASH MAYESH_ ne wanda duk a iyaka daren jiya aka shirya hakan. Kwara ɗayace fara wacce ta kasance bullet proof ce, Duk inda suka gimla sai kaga anabinsu da video kasancewar labarin sarautar madina ba boyayya bace.tuni matasa ƴan zaman banza watk media trend suka fara baza video'n tare da ɗan short rubutu. _kome ya kawo Me girma sarkin madina sarki Ash mayesh zuwa nigeria me girmane don haka I'm waiting_ A jiraye suke dajin kome ke faruwa da abinda ya kawo shi ɗin. Tunfa daga farkon layin har zuwa ƙarshen baka isa ganin iyaka motocin ba, don kuwa bama masu lissafuwa bane dama jama'ar anguwa kuwa harma da wasu anguwannin sun fito dan ganema idonsu dill da dill. Duk kuwa da kasancewar birnine babu ruwan wani da wani to amma wannan batu ake na zaratan sarakuna wanda sukayi zarra sukayi fice a bangaren sarauta. Ganin inda motocin suka fakane yafi jan hankalin jama'a fiye da baya. A cikin masu leƙe kuwa harma da fitowa harda matan gidan. Amma banda Anne su kuwa sunce baza'ayi babu suna ko iyaka motar suka kalla wata rana sun bada labari suce sun taba ganin motocimsa. Saidai me? Tsaiwar da motocin sukayine a gaban ƙofar gidansu suma yaja hankalinsu. Wannan farar motan ita kaɗaice aka shiga da ita har bakin bishiyar settline ɗin dake ta gaban gidan. Wasu zaratan larabawan hadima maine suka kewaye motan tare da fara wata kalan busar sarewa wanda jin wannan busar ne ya sanya Anne tsayawa chakkk domin jinin jikinta taji ya ɗauka wani kalon tsuma tamkar irin wanda yayi kewar wani gi6i daga cikin rayuwarsa loƙaci guda kuma ya samu ko ya gani ko ji haka jikinta ya ɗauka tsuman. Cikin harshen labarci suke kirara wa sarkinsu su kuma fadawan kano na fassara musu, Malam Abdullahi gwani da kanshine ya buɗewa ma sarki Ash mayesh motan. Kyawawan fararen sawayensa da duk tsufa besa sun sanja bane ya fara zirowa cikin wasu shegun almurun bakaken halp cover irin sarakunan nan. Shine ya masa gajora har zuwa babban palon Anne domin yace baya da buƙatar ko ina muhallin Autarsa anan yake da buƙatar ganawa da yarinyansa. Cikin sauri sauran matan suka tari malam Abdullahi suna cewa ya haka duk sauran sassan gidan beyi masa ba sai a sashen Annen kawai zaikai baƙo me girma irin wannan?. "Babu inda mahaifi yafi dacewa da ya gana da ɗiyarsa inda ya wuce ɗakinta!" Wani mugun zabira sukai su duka biyun suna ja da baya tare da faɗin. "Ahhh Rainin hankali dai duk ƙasar nigeria bata isheku wasan kwaikwayon ba saikun haɗa da sarki me girma irin wannnan dan zubar masa da mutumcinsa kome?" Wani kalan yunƙurowa fadawan kano sukay dake sune masu jin duk abinda suke faɗan. muryan da sukaji ya dakatar da sune ya sanya su juyowa su kalli wurin, Ai da wani mugun bala'in gudu sukaja baya suna sandarewa. Don wani mugu mugun kaman..... . _To ai shikenan mu gimtse kawai nima bansan ko miye ba suka hango ɗin_ *BY AMMEY LAYLERH* _MIKIYA_ *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 13&14 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ You Are My Dream Come True _Meerah AK_ Friendship 😊🙃🥰? ?_** Don wani kalan mugun kamannin Anne'n tsantsa da suka gani tattare da wannan kamilallar fuskan dattijon, basu sake rikicewa ba saida queen lajja dake bayan sarki Ash mayesh ta bayyana gabansu itama wanda kai tsaye kamannin Anne'nma duka natane. Ja da baya da baya suke jikinsu na rawan tsoro. Mah (Razeenerh) ce da taji shiru su basuy gaba ba basuyi baya bane ya sanyata leƙo da kanta don ita baki ɗayama tsoron gidan ne ya kamata don gani take taya ace ƴa mafi soyuwa a zukatan iyayensuce ke rayuwa anan wurin. Alhalin su suna can cikin daula da daula ƴarsu na nan na rayuwa a irin wurin nan. "Wllh yau munyi gamo ne Maman Abdallah nafsi nafsi" A haba sai aka shiga tsere tsakanin Matan biyu d0n ganin Mah ɗin ya ƙarasa juyar musu da kai baki ɗaya. Cikin anguwa kuwa kafin kace mene har tayi tafff da jama'a ƴan son ganin dill. Tun tana danne ƙoƙarin danne bugun da zuciyanta ke mata harta gaza dannewa, Raiha ce kwance a gefen Anne'n kasancewan yau weekend ne babu school. Sama take kalla busar sarewan da ake ci gaba dayi na sake bugar da ƙirjinta, Shin sai yaushe ne wai zata dena ire iren waɗan nan mafarkan masu cike da yaudara. don ba yau take ire iren mafarkan ba. Ba yau ba ba jiya ba, ƙofan da taji an taba ne ya sanya zuciyanta bugawa da ƙarfi Malam Abdullahi ne a gaba kafin Mah sai queen lajja me martabane ƙarshe. A nutsenta ta ɗago kanta don gastata kanta. Faɗawa da idonta yayine a cikin wata me balain kama da itane ya sanya jinin jikinta tsinkewa. Tafiya take hannunta yana nuna Anne wasu hawaye na ambaliyan ruwa a saman kyakkyawan fuskanta. "Ke ke kece DIDINA? Lajja wllh Easher'nmu ce wllh itane duk inda jininmu yake baya iya buya don a tafashe yake ba'a daskare yake ba! Har abada jinin Ash ba tauyayye bane ko wacce magudana ta jikinmu tafasa yake jinin mu a tafashe yake Ya abana" Haka Mah ta shiga faɗi tana kuma ƙara kusanta kanta ga Anne, hannu takai da niyar taba Anne'n ai kuwa taja da baya tare da ƙarema ma mah kallo tun daga kan suturar dake jikinta har zuwa ƙarshe. "A ahhh kada hannunki yayi yunƙurin ta6a wannan jikin, gudun kada ki bata naki jikin" "Ka gani ko Abaah ai dama na faɗa ma duk inda jinin Lajja da Ash yake baya taba buya har gaban abada wllh Easher ce itace itace itac......... Sai kuma luuuuuu tayi baya da sauri Raiha ta kwalla ƙara don idonta a kulle suke tin arbar da tayi dasu mah ɗin, ita a zaton tama gamo ne tayi buɗe idonta kuma daidai da faɗuwan da mah ta tafi zatayi. Kafin kowa a cikinsu yayi wani yunƙuri tuni Anneh takai gwiwowinta ƙass mah ɗin ta zube a jikinta,wasu hawayen ta bata san kona miye ba na saƙƙo mata. Da sauri Malam Abdullahi ya juya da niyar fita. "Ina ka nufa yanzun?" Muryan Ash ya katse shi daga shirin fitan da yay niya. "Tana da buƙatan ganin doctor ne" "Ba buƙatan hakan" kai tsaye queen lajja ya kalla tare da furta ki bata taimakon gaggawa" Ko kafin ya rufe bakinsa harta isa garesu ★★★ *KUWAIT* _drems ''Aslm!'' Umaymah ta gajarta sallaman tana tsaye daga bakin parlour'n tana kallon Moh Jiddoh dake zaune akan prey mad, Ahankali moh ɗin ta juyo ta kalleta ko second batayi ba ta ɗauke kanta, zama tayi gefen kujerar da Moh ɗin take Zaune tana ajiye wayarta a kusa da ita tace ''mun kwana lfy Jiddo?" Banza Moh ɗin tamata duk da tajita kuma in da sabo yaci ta saba da halin Jiddon dan mace ce ita mai jin kai har yaranta yiwa take waima a haka ƙaunar umayma'n take. Ringing da wayar moh ɗin ta fara ne yasa ta kalleta miƙewa tayi taje gun dressing mirror ɗin ta ɗauko mata Asaad ne me ƙiran wanda t take kira Autan ta dake England miƙa mata wayan tayi ta gagaya tana zama tare da ɗaukar tata wayar whatsApp ta shiga tana duba messages kallon message ɗin data turama Autarta yasmine tun friday da dare ta kalla, yanzun madai ganan alaman kore alamun har duba message ɗin tati kenan. Amma ta ƙi bata amsa _Hii Yesmeern lafiyan?_ Ta sake tura mata kuma yayi two tick kuma ta gan story ɗinta amma bata duba message ɗin nata ba sauƙa tayi tare da switch data'nta tayi ma baki ɗaya. Maganar da Moh tayi ne ya sanyata maida dukkan hankalinta thought bata ɗago kai ba akan Moh ɗin ''uhm Umaymah kenan ae shiyasa naso tun a wancan loƙacin naso mu gama da komai amma abun ya gagara gashi kuma a halin da ake ciki yanzun babu damar hakan!'' shiru Umaymah tayi na ƴan seconds da alama tana sauraren abunda Moh jiddoh ɗin ke faɗa mata ne ''Duk da ance shi icce tun yana ɗanyensa ake iya lanƙwashi, to amma ni duk da bushe ɗin zan iya lanƙwashin! Idanma ta kama da karyewa to kuwa karyashin zanyi don buƙatan kaina ya biya Moh'' duk da a karkace tayi maganar amma tasan inda maganar ta dosa. Murmushin gefen baki moh ta saki sai ta ɗago batare da nuna komai ba ta furta "Uhmmm dakyau ki kula sosae wajen lankwasar dai kar yazam mu ta sake kwabewa" Wani kallo ta jefa mata wanda kai tsaye jiddon ke ankare da ita, itama wani shegen murmushi tayi ita kaɗai tasan abinda take kwancewa da saƙawa. "Zan kula sosae karkj damu Jiddoh komai zai tafi a tsarinane tafiya a tsarina kuma baya nufin kwa6ewar aiki irin na wasu!" Kai tsaye jiddo tasan maganar nata ne kuma ta amsa kamar yadda umayman ke buƙata dama, "Aha Allah temaka na ce saimun sake haɗuwa". Dama kamar jira umayman take ko irin wacce take akan ƙayar nan haka ta miƙe zimbir tana barin parlou'rn a zuciyarta take faɗin. {Mayyar mata kawai kullum tana kan sallaya kamar wata mutuniyar kirki nan kuwa sai shegen iya ƙulla makirci da haɗa tuggun tsiya...} Tana tafe tana duba wayanta loƙaci bayan loƙaci kuma tana jan tsuka, kamar daga sama kuma sai ganin ƙiran yasmine tayi ya shigo wayanta. Saurin peak call in tayi gudun kada ta katse mata ƙira don tasan kaɗan ne daga cikin aikin Yasmine ɗin. Daga ta can bangaren cikin harshen larabci yasmine ta furta. "Hala akwai abinda yake tafiya ba daidai ba tunda naga saƙonninki harta email!ok?" "Loƙacin zamanki America ya ƙare yasmine don loƙacin fara farautane wannan! Amma ya kamata ki taho haka nan my be not my be forever kuma" "Kina nufin A maleek na Emaar's a yanxun haka Mommah?" "Yana a harma da tsarabnan wifey a tare dashi" Daga kwancen da take ta mike tsaye zimbir tare da faɗin "Ma me? Kamar fa mata naji kin ambata mom a taya A maleek zaiyi min haka? Shikenan kitsimayi zuwana Later" Daga haka ta datse ƙiran tare da dafe kanta da taji loƙaci guda ya balain sara mata. "A wannan karon dole ka faɗa hannuna Abdoul-Maleek Emaar's ko kaki ko kaso mata ne bisa kanka wanda ake mana laƙabi da gangar shaiɗan" _Amma wait! Nidai nace babu ni Ammey Laylerh tare da duk me karanta littafin Mikiya Uhummmmm_ ★★★ _Some late_ Karon dataci da wani abu kamar gini ne yasata saurin ɗagowa tana yin one step back hannunta dafe da hancinta data buge tare da forehead ɗinta amma hancin yafi mata azaba A hankali ta soma ɗagowa dan son tabbatarma kanta wanda ke tsayen saboda wannan unique ƙamshin da bata ta6a jinsa jikin kowa ba sai jikinsa ɗin. Kallon kallo sukewa juna ita dashi kasancewar sa mutum mai tsayi sosai kuma dai kunsan tsawon mace dana namiji yanda suke hakan yasa ta koma wata ƴar karama. ''Halan kai makaho ne?'' da ƙarfi tayi maganar dan ganin yanda yawani mata tsaye a gaba tamkar wani bijimin sa. Idan inda suke tsaye yayi magana to shima Ak yayi, jin yaƙi ko tanka mata ne ya sanyata sake faɗin ''Malam nace baka gani ne? kokuwa iccen daka buge baiji maka ciwo ba?'' ta faɗa tana hayayyaƙo may ta buɗe baki kenan da niyar sake magana muryan Jesrah ta dake tahowa ta katseta. Cikin shegen rainin hankali ya dubi jesrah tare da faɗin''dalla malama hold it na ce miye wannan aka kawowa mutane gida'' da sauri jesrah ta duba ak ɗin tare da faɗin ''Akie Merrah ne fa'' Wani kalan yamutsa fuska yayi tare da furta''miye wani Merrah kuma?'' yanda Yake yatsina fuska kamar yaga kashi ne sake hasala Meerah ɗin itama. ''Akiey Matarkane fa wanda aka ɗaura ma aure da ita already tuni'' wani irin shegen murmushi yayi yana yuja kai ya tabe baki irin anzo wajen Nan. ''Au cemin zakiy kaskar data maƙale tace saini, wacce tabi duk wani lungo da saƙo don ganin ta shigo rayuwana. Fine amma bara na tuna miki wani abinda basu faɗamiki ba nan gidan ba kowane mara aji ko jani talau ne yake iya shiga ba bar ganin kin samu shigowa fitan ma ba wahalan zaiyi ba kamar shigowanki EMAAR's...... Ɗagowa Merrah tayi a karo na farko tunda suke tsayen ta kalleshi straight in the eye. Tare da furta. "Who are you? How dere you?" Ta faɗi in a low dangerous voice, kafin taci gaba da faɗin. "Saidai gidan ma ai beyi kama dana mutane tunda ba'a daidai ɗinsa yake ba, Kuma a kallon farko ma gidan beyi kama da gidan da mutane ke rayuwa a cikinsaba baki ɗaya duhu da duhuwa ne kewaye da durƙushashshen kangon ginin daya yake a baybay" Da wani kalan kallo ya bita me kama dana rainin hankalin nan. "Idan ma dalilin wani abu yasa kika nace saikin shigo gidan nan toh ki sani bakida muhalli a yanzu dan the house is full with children's no more room for you'' Yana faɗin hakan ya wuce abinsa bayan ya mata wanna shegiyar alaman datafi tsana fiye da komai daga gareshi. "Babu wanda besan halin Akiey ba so inaga hakan ba abinda damuwa bane dear!" Taji muryan jesrah tana jan hannunta lips nata taɗan ciza bada yawa ba tana bin bayan jesran don dama wurin oum suka nufa data aiko ƙiranta. Oum ɗin ta tarar zaune tare da jesrah wacce ta labartama oum ɗin komai daya faru. Cikin ƙarfin halin Oum tace "$higo man Meerah kinzo kin tsaya a Kofa? Zonan kusa dani kinji ta faɗa tare da nuna mata gefen da take zaune,murmushi ta yi tare da karaso ta zauna kusa da itah kamar yadda oum ɗin ta buƙata ta sunkuyar da kanta ƙasa tare da faɗin. "Oum good afternoon" Murmushi Oum ta saki tare da da amsata da "Lafiya Alhamdulillah baki biyo bayan iyayenki nema zance ns ko kakanni nema" Ɗan murmushi kawai meerah ta saki tana jinta a takure da zaman da sukeyi ɗin, dan har yanzu ta gaza sakin jikinta da oum don sosai take kunyar matan yanzun ma jinta take kamar ta gudu haka taji aranta. "Jesrah kuje ku gaida mutanen cikin gidan" "Tomm Oummuh" Jesran ta faɗi ko kafin ta miƙe kuwa tuni zaram har meerah ta rigata miƙewarma, kai tsaye bangaren Umaymah jesrah ta fara raka Meerah ɗin. da wannan shegen makircin nata da zagon ƙasa ta tar6esu faran² Allah'n baka. Basu wani jima ba sosae suka mata sallama wasu manyan arabian jallabiya tare da Alkyabba da turaruka masu tsada sosae ta haɗa meerah dasu. Ko kallon kayan batai ba jesra ne ta amsa tana mata godiya. Daga nan bangaren Moh jiddoh suka yi a loƙacin tana zaune ne akan caution tayi crossing ƙafafunta tana karkaɗasu idanunta a lumshe ita kaɗai tana aikin saƙawa da kwancewa. Wani kalan buɗe idonta tayi tare da juyowa zuwa wani mummunar faduwa gaban moh jiddoh yayi zuciyarta ya shiga harbawa da sauri-sauri idanu ta rufe ganin wani irin haske mai bala'in karfi ta cikin idanun meerah ɗin batayi auni ba taji muryarta na cewa "Innalillah wa'inna ilaihir raji'un meke shirin faruwa dani ne haka ni jiddoh yau na shiga uku!" Da sauri jesrah ta fita a ɗakin tana cema Meerah tana ɗan zuwa don wayan da aka ƙirata. Wata nannauyar ijiyar zuciya Moh ta sauƙe tare da furta "wllh shegiyar yarinyar nan tsoro ta bani kodan jinin mayuce masu shegen ƙarfi jinin tsiya tirrr dai wllh har abada ba'a taba sarki biyu a guri ɗaya" tayi maganan tare da buɗe idonta ba kuwa su faɗa ko ina ba sai cikin na meerah. Baki ta buɗe mata tare da daƙune fuskanta sai kuma gata zaram akan jiddon. "Da kina yarinya bakiy karatu bane? Cokali ɗaya na nonon sa yafi daro ɗaya na nonon jaki, uhmmmm dama saida nai tantamar ba'aje makaranta ba. duk aukin jakuna ba zasu taba kama ƙafar doki a gudu ba. Kuma har abada zakara shi kaɗaine sarki Moh ɗinmu ta ƴan gayu" Ta waske abinta tana kamar gyara mata rufin hulan kanta tayi ganin shigowar jesrah. Saƙeƙe haka moh tayi tana me bin meerah da ido kawai fakar idon jesran tayi tare da ƙyafta mata ido ɗaya da kashewa. "Ina ganin mutafi haka nan ko dear?" "Ehhhhh hakan ma yayi. Moh sai haɗuwa ta gaba yanzu ta wuce sauri muke ki kwana cikin sauƙin zuciya Allah kuma yaja da ranki kisha kallo my kakas" (Yau naga yadda ake bariki ni mai jiddah, to kodai akwai abinda yake ba daidai ba ko yake a baybay bana da masaniyar hakan kuma?) Ta ayyana a zuciyarta tana jinjina ƙarfin halin yarinyar, {kai ina wllh ma tana da aljanu yarin yarnan} ta sake maimaitawa tana faɗawa bedroom nata. Haka Moh ta kwana datunanin abunda ya faru tsakaninta da Meerah sosai abun ya tsaya mata a rai,tunda take bata ta6a ganin makaman cin haka ba a iya tsawon rayuwarta duk me hakan ke nufi?, ya zama dole ta shirya ma zuwan waɗan nan jerin abubuwane ma zata ce ko ƙaddarori ne ma oho da wanan tarin tunanin bacci ya ɗauketa. A ta bangaren meerah kwana tayi da tarin abubuwa maban banta wanda suka farun min dama wanda suke kan faruwan. Ruɗani,mamaki, al'ajabi sun taru sun hana Meerah runtsawa a wannan dare. Kanta ya gama kullewa dangane da abinda duk suka faru ɗazun tsakaninta da Moh da kuwa wannan Aljanin. Shin mutumin nan ɗan dabar ne da gaske? Kokuwa wani abu daban da bata sani ba. Babu abinda ke mata kaikawo a zuciya sai kalan yadda ya ringa yaba mata maganganu da kuma haɗuwarsu na jiya daya bita har ɗakin ta me hakan ke nufi kenan? Ita kam al'amarin wannan gida ya fara birkita mata lissafi tun a farkon shigarta komai ya gama bayyana kansa gareta. A lissafin ta dai Moh jiddoh itace uwar masu gidan to amma ta ya ya Akai ta kasance me fuska biyu. Abubuwa sosea ya hango tattare da matar baƙaƙe ba masu lissafuwa ba. Zuciyarta a ƙone take babu ko ɗigon rahama idan har lissafinta ya bata daidai Kenan 6atar da Annenta akayi a cikin wannan masarautar? A tunaninsu ita ƴar gidan ce kenan miye silar mutuwan matan me martaba ga biyu? Zancen daya faɗa a baybay ita tuni ta gama fayyace abinta filla filla tun a ranar. Kuma ita kaɗai tasan abinda taga ni ta kuma ɗaukarma kanta alƙawarin bibiyar kowa da kowa na wannan masarautar har zuwa kan dalilin da yay bacewar annenta. Kenan Anne ita bama ƴar nig bace Sarki Ash dai shine cikakken mahaifinta Allahu ahaad lallai Allah da girma yake. ? Sai wajajen ƙarfe biyun dare bacci yay ciki da ita cike da tarin wasu mafarkai masu ban tsoro. A hankali hasken rana ya bayyana a sararin samani. Wanda haka yayi dai-dai da farkawanta tare da bayyanan ciwon da taji maranta ya harba mata, ya mamaye duka har sassan jikinta da zuciyarta. Wani irin rumtse idonta tayi tare da tashi zaune cikin wani irin gigitaccen ciwon da ya mata dirarn farat ɗaya tace. "Sheehhhhhhh Wayyo! wayyo!! wayyo Allah Anne na ciwo zafi wayyo Raiha wayyo kowa da kowa na cikin duniyar ma baki ɗaya. Wayyooooo" Ta faɗi da ƙarfin daya farkan da jesrah a zabure don babu jimawa da komawansu bacci bayan sunyi sallar subhi. "Subhanallahi Aunty meerah mike faruwa?" ta tambayeta cikin muryan bacci tana mikewa tare da nufo wurinta, wani irin juyi haɗi da murƙususu meerah keyi wanda hakan kai tsaye ya sake firgitar da jesrah kai tsaye ta fita a dakin da gudunta domin sanarma da Oum. ★★.....★★★ A ta bangaren umaymah tun a daren jiya ta gama shirya komai na tarbar dolky'nta tun daga kan abincin da takeci har zuwa tsaftar sashen ma a yau ta kasance ta musamman duk da a kullum a tsaftace yake. An shirya kalolin abinci da ƙamshinsu ya gama cika ko'ina na sashen har maƙwaftan shashen ma ka iya jiyowa. Duk ata dalilin son ta farantama dolly'n. A mugun guje rantsatsiyar baka wulik ɗin lafiyayyar motar da dolly ke ciki ta tsaya gab da ƙofar shashen umaymah, cikin rawar jiki ɗaya daga cikin Hadiman ya buɗe mata motan, sauran kuwa tuni sun zube ƙasa kan gwiyawunsu kawunansu a ƙasa domin kai tsaye sun san dokar madame dolly'n DA'DAH. Tun a farkon shigowan motanta kuwa cikin Mention ɗin hadima suka dinga tsere don gujema haɗuwa da ita bare takai ga yi mata laifi. A ƙalla taja Sama da mintuna goma batafito ba duk da kasancewar an buɗe mata, sai da taga dama dan kanta sannan ta ziro ƙafarta fara tas dake a cikin ƙyaƙyƙyawan blue ɗin takalmi mai tsananin taushi da ɗaukar ido da zai iya birge duk wani mai kallo, Wanda yaci uban naɗi da igiyoyin dake jiki, kusan sakan biyar a tsakani sannan ta ƙara zuro ɗayar cike da ƙasaita. Tashin ƙamshin turarenta da takun sawayenta ya tabbatar ma duk wani rai mai numfashi ata bangaren isowarta. Wanda hakan kai tsaye ke sanya su rusuna kawunansu ƙass gudun haɗa ido da ita kayi laifi. Cikin wani shegen taku take wucesu hancinta ɗage a sama tana wani huhhurashi sama ita ga ƴar zafin kai. Wasu shegun ɗamammun riga da wando ne a jikinta na jeans iya ma'alwantarta kan nan naɗe cikin swear band me shegen kyau da tsaɗa, da wani irin maɗaukakin farin ciki umaymah dake zaune ta miƙe tana rungumar yarin yar nata. Kafin da hannu taima dukkan amintattun hadimanta dake zagaye da ita nunin su fice. Har rige-rigen bin ƙofar da zata kaisu falon farko dazai fiddasu ta ainahin ƙofar sashen nata suke. "I miss u my dolly'n Dada" Wani iska taja tare da jan numfashi ta fesar a hankali. Idanunta ta ɗan ƙankance da jinjina kanta tana sakin ɗan karamin murmushi domin Dada ɗinta da tafi kewa fiye da komai har ita kanta momman kuwa. Ita kuwa Umaymah da take jin duk wannan ranar tanajinta rana ta musamman ne a gareta, sakar mata kiss a goshinta haɗi da zaunar da ita tamkar bata baby. "Mommah Kina lafiya?". "A zahiri dai lafiya nake, amma a baɗini cike nake da tarin damur dake cinkushe a raina first" Umayman ta faɗi fuskanta na sauyawa daga yanayin farin cikin da take ciki zuwa kishiyarta. "Uhhm!" Yasmine ta faɗa da ɗan lumshe idanunta ta buɗe Still a lokaci guda. "Kai tsaye ki faɗin damuwar don nima yanzun haka a cikinta nake saidai jin wannan lamarin ya shafe wancan ɗin don shi serious bane kamar wannan ɗin" Kai tsaye ta ɗan tsaƙuri lamarin a ciki ta bata. Idanunta a lumshe suke buɗesu tayi tare da fesar da numfashi ba tare data bata amsan tambayar data mata ba ta furta. "DADA fa?". Tay maganar a fisge tamkar yinta ya zama tilas ne a gareta. "Yana mashel kotra" Wani kalan zaro idonta tayi wanda suke a bugu wanda kai tsaye inkai mai fashimtane a take zaka fahimci ba'a daidai suke ba. "Be dena zuwa Mashel kotra ba har yanzun kenan?" ???........... *BY AMMEY LAYLERH*