[8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *♡ME ZAN YI DA ITA?♡* NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 Da sanyin safiya ta fito daga rugar fulanin cikin wata bukka dake daga gefen rugar sanye take da kayan fulani irin usul din fulanin nan fuskarta a cunkushe da mabayyanin ‘bacin rai. Tana tafe tana kunkuni alamar ba dan son ranta ya fito ba. Kwarya ce a kanta da nono a ciki a tsakar gidan ta tarar da mahaifiyarta zaune da turtsesten ciki a gabanta ta had’a kai da gwiwa . Har zata wuce sai kuma ta dawo ta tsaya mata’kerere a ka, bakinta a zun’bure tace “innaji zan tafi” innaji ta saki ajiyar zuciya kafin ta furta “idan kinje ki gaida modibbon saura kuma idan kin fita ki tsaya dukan d’iyoyin jama’a ko tumakinsu “ “ aradu duk yaran da ya higa gonata nima sai na higa ta uwarshi “ cikin takaici innaji ya watsa mata harara “ ina magana shatu kina cewa aradu sai kinyi to ai shikkenan kije kiyi Allah ya shiryeki ni dai ina gaya miki ki kula da kanki kina sani ba kowa ne damu a garinnan ba idan mune yau fa anjima gawa muke bana son ace har yanzu kina wannan halinnaki kowa unguwar nan yasan halinki ba mai fad’ar alherinki sai aibunki shatu don Allah ki shiryu kada kizo nan gaba kina wahala a lokacin da ‘kasa ta rufe min ido “ . Duk da jikinta yayi sanyi bata fasa cewa “yo innaji sai na bari yara suna tsokanata suna ce min mai idon mujiya kamar ubansu ya rad’a min “ innaji ta mi’ke da kyar da alama cikin yayi mata nauyi murya can ‘kasa ya kama hannunta “ suyi ta fad’a miki mana kyau idanun suke musu masha Allah zaki dinga cewa idan suka fad’a miki yi sauri ki tafi kinga hadari na hadowa ki gaidar min da modibbo ki kar’bo min rubutun idan ya rubuta “. Da sauri ta fice kamar zata tashi sama tana ayyana “ wallahi innaji ba zan kyalesu ba jibgar d’iya ni kayi idan ya shiga gonata’yan kwal uba masu kan faranti “. Da tsallanta take tafe da wa’karta duk da ‘kwaryar nonon da take kanta har da cilla sanda duk yaran da ta wuce’kus suke da bakinsu kada suyi magana suci Na jaki sai dai tana wucewa suke tuntsira dariya murya ‘kasa’kasa suke cewa “mujiya idonki a loko “ sai su taka da gudu. Shatu ‘kwafa take tana haddacesu d’aya bayan d’aya ta kuma tabbatar wallahi sai sunyi bayani. A saman buzu ta tarar da kakanta Na gurin uba moddibo wanda ya kasance gawurtaccen malami a garin nutsuwa tayi sosai don shi kad’ai take tsoro a garin , ta ra’be gefensa ta tsuguna sai da ya kai aya sannan ya d’ago ya kalleta fuskarsa ba yabo ba fallasa yake amsa gaisuwar da take masa “ Gashi inji innaji tace tana gaidaka “ moddibo ya girgiza kai had’e da jan’kwaryar yana girgiza kai “ ‘yar nema ai Na zata yau ma kinyi halinnaki kin zubar dashi wallahi da yau ma sai na zaneki dan na lura sam ke baki tausayin innarki idonki a tsakar ka yake d’auki ki kaiwa salame Ta adana shi a ciki” mi’kewa tayi zuciyarta a tunzire kamar ta kai masa mari ita fa ta tsaneshi bata ‘ki ya she’ka barzahu ba don ya takura mata baki kamar shantu ta fad’a a zuciyarta zanyi maganinka aradu gobe. A tsakar turken tumaki ta tarar da ita salame ta amsa gaisuwarta tana kar’bar’kwaryar nonon fuska a sake tace “ya jikin innar taki?” “ ba sauki sai na Allah yo wannan uban ciki yayi mata turtsitsi ta ina zata samu sau’ki Idan ba haifeshi tayi ba aradu duk ranar da Ta haife abin da yake cikinta sai na jibgeshi “ salame ta zaro ido tana kallon shatu da take zaro zance “ashe kuwa dai shatu da ake cewa baki da kai zancen ya kusa tabbata jaririn zaki jibga?” Ta ta’be baki “ yo idan ban jibgehi ba ai aradu ban haifu ba a cikin innaji ko sallah fa a zaune take yi gashi tun a ciki shegen karanbani garai yayi ta kwarafniya jiya fa ina kallon cikin yana wutsilniya wallahi tana cin abinci kika ji d’if tun kan yazo duniya ma ya nuna halinsa” salame ta girgiza kai tana katse’kwaryar ta mi’ka mata daidai lokacin da modibbo ya shigo yana dogara sanda “ to uwar shashashanci kina nan kina zuba kamar ‘ya’yan kanya zo ki wuce ki kai mata rubutun Allah ya raba lafiya” “ ameen “ ta furta murya can ‘kasa “ ai kai na gado a kwakwazo duk gari an sani” mai kika ce “? A guje ta arce tana fad’in cewa nayi Allah ya tashe mu lafiya salame kuwa girgiza kai tayi don ita taji abinda tace sarai don dai shi ma kunnensa yana da matsala ne. Tun a hanya take Allah-Allah taga d’aya daga cikin yarannan sai dai bata gansu ba haka ta koma gida ranta a ‘bace da rashin cikar burinta. Tana shiga innaji ta kar’bi rubutun had’e da nuna mata buta ta san nufin innaji tunda lazimi take ta sunkuci butar ta fara alwalar. A nutse ta tada sallah duk da rashin jinta innaji Ta tsaya sosai wajen bata ilimin addini don masaniyace sosai Na boko ne dai sai taga dama take zuwa ko idan an tura ta ta shige gonakin jama’a tayi’barna. Suna idar da sallah innaji ta ri’ke hannunta murya a raunane tace “ shatu jikina yana bani kamar rayuwata tazo gangara don haka ya zama dole yanzu Na sanar dake labarina ko da nan gaba zaki bu’kaci haka a lokacin da ‘kasa ta rufe min ido ga mahaifinki tsawon wata biyar da tafiyarsa har yau ba amo ba labari daga tafiya fatauci ina son ganinsa ban san ina ya tafi ba.” Hawayene ya ciko a idanun shatu sam bata son taji innaji tayi mata zancen mutuwa ta lura kuma kwana biyu kullum zancenta kenan. “ innaji don Allah ki daina min zancen mutuwa idan kika mutu an higa uku “ baki shiga uku ba shatu Allah yana tare dake kuma kina da gata tunda moddibo yana raye balle nasan mahaifinki komai dad’ewa Zai dawo ki share hawayenki burina kawai ki nutsu “ fad’awa jikinta tayi “don Allah ki daina cewa zaki mutu ni kece gatana “ innaji murmushi tayi tana kallon zallar yarinta a idon shatu da Ba zata gaza shekara sha daya ba. “ To ki dinga addu’a Allah ya rabamu da cikinnan lafiya naga aurenki shatu “. Da sauri ta furta ameen “ Har dare tana son jin labarin da innaji zata bata amma kuma tana tsoron zancen mutuwa don haka tayi mu’kus. Cikin dare ta kasa ha’kuri ta mi’ke zaune “Innaji baki bani labarin ba “ murmushi innaji tayi don tasan shatu da son jin zance ta mi’ke zaune da ‘kyar ta jingina da bango. *********. ********** Asalina haifaffiyar garin liman katagum agarin bauchin yakubu sai dai mahaifiyata yar asalin mambilace a jihar yola acan mahaifina ya ganota ya aura shi yasa zaki ganmu da asalin kyau na fulanin usuli. Mahaifina d’an bokone mu biyu iyayena suka haifa daga ni sai yaya ta dijama. Kasancewar mahaifina lecturer hakan yasa ya dage akan harkar iliminmu. Muka taso cikin tarbiyya da ‘kaunar juna ni da yayata mai tsananin kama dani ta girme ni da shekara hud’u. Yayata tana gama secondary samari su kayi mata ca hakan yasa babanmu yace dole ta fitar da miji duk da kasancewarsa d’an boko baya take ilimin addini yana bashi ha’kkinsa sosai. A lokacin ina ss 1 yayata ta fitar da miji a kayi mata aure da wani matashin mai kud’i ahmad manga inda suka tare cikin garin bauchi a unguwar gwallaga. Lokacin da na shiga ss2 a lokacin muka fara soyayya da wani ma aikacin makarantar atbu inda gidanmu yake kasancwar a staff houses muke shara yake da gyaran compound d’in gidanmu soyayyarsa ta d’ibeni don kyakykyawa ne sosai . Ba wanda ya sani a gidanmu a ‘boye muke komai duk da bama keta iyakar ubangiji amma fa soyayya tayi zurfi a tsakaninmu ta yarda tabbas a lokacin idan aka hanamu aure zamu iya rasa rayuwarmu. Duk da bashi da ilimi haka nake son shi tunda yana da ilimin addini bokon ma a hankali nake koya masa a ba ca da. Ina ss 3 tashin hankalin ya fara zuwa don kuwa wani d’an abokin babanmu yace yana so na babanmu kuma yace ya bashi gashi bababnmu irin masu kafiyar nan ne sam baya juyuwa mai juyashi dama babansa ne kuma ya rasu. Hankalina ya tashi sosai nayi kuka kamar raina zai fita na gaya wa mamanmu bana sonsa ta fad’awa baba yace ban isa ba bai haifi dan da zai ce yes yace no ba. Haka mamanmu tayi ta rarrashina ita da yayata amma zuciyata Ta kasa ha’kura. Hakan ya tunzira zuciyar Baba yace ya fasa barin sai na gama jarrabawar na ‘karasa a gidan mijina aure zai yi min. Aka fara shirin biki hankalinmu a tashe ni da miji wannan yasa ana gobe d’aurin auren muka gudu ni da miji. Da sassafe muka wayi gari a wata ruga ya bani kayan fulani na saka sai da muka zo gidan ya sanar dani gidansu ne nan ya shiryawa mahaifinsa ‘karya akan cewa iyayena sun rasu a hanya kuma fulanin tashi ne hakan yasa suka rungumeni a gidan bayan wata biyu aka d’aura mana aure da miji duk da kullum zuciyata na bani shawarar na koma gida amma ina tsoron mahaifina. Shakararmu goma da aure kafin Allah ya kawo cikinki. Har yau a garin nnan ba wanda yasan ina da ‘yan uwa sai yanzu da nake gaya miki kina zuwa liman katagum kika tambayi gidan sarkin fulani nan ne main house na familyn babanmu koda ta Allah zata kasance. Ya fad’a hawaye na ziraro mata na tuno iyayenta. Shatu ma hawayen take “yanzu innaji da gatanki muke ta yawo bama nan garin bama can mune har nan niger 🇳🇪 ashe asalinmu yan nigeria 🇳🇬 ne “. Innaji ta dafa kanta tace “kaddarar haihuwarki ne shatu da ta wannan cikin fatana idan kin sadu da dangina kice su yafe min na mutu ina tsananin kewarsu “. Share hawayenta tayi tace “insha Allah innaji ba zaki mutu ba da ‘kafarki zaki ga danginki “. [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 - 2 Sumul suka farka innaji ranar ta d’an ji sau’ki, har yamma shatu na tare da ita Ta kasa motsawa ko nan da can ranar kam jikinta a sanyaye yake duk tsiwar da masifat ta zubar tana gefen innaji a zaune kan tabarmar karauni. Innajin Ta tsefe mata kanta Ta wanke tas da kanwa da karkashi sai ‘kyalli gashin yake yasha man kwakwa kasancewar shatu mai gashi na ban mamaki tamkar mutanen ‘kasar hindu don ma bata son gyarashi da ‘kyar take barin innajin ta ta’ba mata kai shima sai tayi mata jan ido. Har aka gama tana kwance lamo ba mai magana tsakaninsu ita innaji tana karatun suratu maryama ita kuwa shatu ta lula duniyar tunani gaba d’aya ta rasa sukuni.har la’asar tayi kafin ta mi’ke tayi alwala ta kuma zubawa innajin ruwan alwala innaji ta kar’ba tana murmushi “ Allah yayi miki albarka shatu yasa ki cimma duk burin da nake miki fata a rayuwarki “. “Ameen “ shatu ta fad’a murya a sha’ke. Suna idarwa innajin ta aiketa gidan modibbo kar’bo rubutu. Duk tsokanar da yara suke mata a hanya ranar banza tayi dasu burinta taje ta dawo ta iske innaji lafiya sumul, don haka take ta sauri kamar zata tashi sama. Ko mintuna biyu bata yi ba a gidan moddibon ta juyo a sukwane ko saurarar gwaggoji ( salame) da take ‘kwala mata kira ba tayi ba. Kamar an cillota haka ta afka tsakargidan da sauri ta saki ajiyar zuciya had’e da cewa Alhamdulillah Allah innaji na d’auka kafin na dawo kin mutu” murmushi innaji tayi kafin ta furta “mutuwa ai sai lokaci yayi ayshatu” da sauri ta dubeta jin sunan da ta kira ta dashi innaji ta waro ido tace “lafiya “ ta hau girgiza kai “ ji nayi kin kira ni da sunan da baki Ta’ba kira na ba “ dariya kawai tayi tana shan rubutun ta had’e da kallon shatu kallo mai nuna tsananin ‘kaunar da take mata. Cikin dare innaji ta fara jin ciwon na’kuda tun tana daurewa har abin yaci ‘karfinta ta mi’ke da ‘kyar ta bud’e wata adaka ta zaro wasu hotuna da biro ta rubuta address din family house d’insu ta nad’e a takarda ko bakomai bata san ya ta Allah zata kasance ba. Da ‘karfi ciwon yazo mata har bata san lokacin data fara tashin shatu ba a razane shatu ta tashi saboda wani mummunan mafarki da take a wannan lokacin, ganin innaji cikin wani mawuyacin hali bata san sanda ta zunduma ihu ba tana ru’kun’kumeta “ bana so innaaji bana son mafarkin da nayi ya tabbata “. Da kyar innaji ta’ka’kalo wani murmushi tana mi’ka mata takarda “ ayshatu ban san ya ta Allah zata kasance ba amma koma dai yayane bayan raina ki nemi dangi na idan mahaifana suna raye ki basu wannan takardar da wannan hoton suna gani sun san ke jini nace Ayshatu idan babanki ya dawo kice masa ya yafe ni Allah ya yanke ganawarmu “. Hawaye take yi sosai na tsananin azabar na’kuda. Ayshatu kuwa ta zama kamar mutum mutumi ta rasa ma mai zatayi abinka da’kan’kantar shekaru. Sai jijjiga innaji take ba bakin magana har zuwa sanda taji innajin ta saki kalmar shahada jikinta gaba d’aya ya saki ji kake d’if lamarin Alhakamu ya tabbata. Ita kuwa a nata tunanin barci innaji tayi bata san mutuwa ba bata san ya ake mutuwa ba gashi ana fad’a musu zafin fitar rai a yanda kuwa ake kwatantawa tabbas wannan ba mutuwa bace barcine ta ayyana hakan a ranta, don haka hankalinta kwance ita ma ta kwanta a gefen innajin barci ya kwasheta barcin da shine ya kaita har’karfe goma na safe. Tana farkawa ta tashi a razane tana kallon hasken d’akin tare da tunanin me yasa innaji yau bata tashesu sallahr asuba ba. dubanta ta kai inda innajin take da sauri ta zare ido ganin idonta a kakkafe ya kalli sama ai bata san sanda ta hau jijjigata ba jin bata motsi yasa ta runtuma waje a guje tana Kiran jama’a “kuzo ku duba min innata tayi barcin zomo na tasheta ta’ki tashi “ ma’kota suka shiga gidan sai gani tayi suna fitowa jiki a salu’be ga kallon tausayi suna mata . Kalmar da taji wata ta fad’a ne Allah yaji’kanki maryamu halinki na gari ya biki yasa ta farka daga tunanin da take na cewa innaji barci take.aiko zuba hannu aka ta ‘kwalla’kara sai ganinta a kayi a zube ba numfashi. Allahu akbar kabeeran Ubangiji kenan mai yin yarda yaso a lokacin da yaga dama Allah yaji’kan iyayenmu. A safiyar juma’ar misalin ‘karfe sha d’aya na safe aka sada innaji zuwa gidanta na gaskiya hawaye sai zarya yake a fuskar abokan arziki kowa ya shaida innaji bata da abokin rigima to ita maganar ma bata dameta ba balle har ta samu abokin rigima. Shatu zube a cinyar gwaggoji sai mayar da ajiyar zuciya take da razana har sai da moddibo ya sake mata rubutu aka bata. To haka dama rayuwa take. A hankali shatu ta fara sabawa da rashin innaji kullum kuwa ma’kale da takarda da hotunannan take kwana tayi al’kawarin sai ta sadu da dangin mahaifinta. Gidansu gwaggoji ta koma ta daina wanka ta daina komai wai ita ta gama jin dad’in duniya tunda innaji ta tafi ta barta. Yaran mutane kuwa a lokacin ta ‘kara takura musu musammam masu uwa raye shatu bata da ‘kiba sam amma sai ‘karfi ta gallabi mutanen garin tun ana d’aga mata’kafa saboda rashin uwa har tausayin ya kau aka fara kawo ‘kararta wajen gwaggoji. Gwaggoji bata da fad’a sam don haka shatu take’kara sangarcewa kullum da rashin jin da zata rakito ta kai yanzu har manya shiga shirginsu take musamman masu gonaki da suke kuka da ita. Makaranta kuwa tuni tayi sallama da ita ta allo kawai take yi itama don moddibo yana cin gidansu ne da batayi ba. Gashi yanzu shi bashi da cikakkiyar lafiya yau fari gobe tsumma. BAYAN WATA SHIDDA Da rasuwar innaji jikin moddibo ya ‘kara tsananta, hakan yasa shi fara had’a komatsansa baya so ya mutu anan ya fito ya mutu cikin ahalinsa da suke garin yola. Itama gwaggoji hankalinta yafi kwanciya su tafi musamman saboda shatu ko bakomai a can dangi da yawa za’a samu mai tayasu kula da ita. Safiyar wata asabar suka fito da ‘yan ‘kullin kayansu suka fara sallama da mutanen garin da suka yi dandazo a ‘kofar gida, duk jikinsu yayi sanyi musamman yara da suke kallon shatu Idanunsu fal ‘kwalla. Shatun ma kuka take ta kalli yaran tana murmushi “kuyi min tsokanar’karshe don Allah ko bakomai zan dinga tuna ku.” Shiru su kayi mata, murya na rawa ta fara binsu d’aya bayan d’aya tana cewa “ku fad’a mujiya mai idonta a loko....” Ai kuwa yara suka fara har ita suna kuka kuka, dariya- dariya a haka suka rakasu har inda mai amalanke yazo ya d’ebesu tana d’aga musu hannu suna bin amalanke , rayuwa kenan ba mamaki shikkenan tayi sallama da garin nijar. Amma ta’kudirce insha Allah zata dawo. Kwanansu kusan biyu suna tafiya, kafin Allah ya kawo su garin yola nan suka hau motar garinsu demsa, daga demsa suka shiga wata’kur’kura ta isar dasu cikin ‘kauyensu gwamba. Ai kuwa mutanen garin suna ganinsu suka shiga fitowa ana murnar ganinsu. Bayan sun shiga cikin gidan mai girman gaske ginin’kasa suka fara yiwa juna gaisuwa anan suke jin labarin mutuwar muji mahaifin shatu. Ashe da ya taho hatsari yayi a garin yola hakan yasa ya bada address din family house d’insu na nan kafin a kawo shi kuma rai yayi halinsa. Su kuma basu san inda zasu samesu ba. hankalin shatu ya tashi ta zube wajen har iskokanta suka ziyarceta, kowa a wajen ya tausaya mata musamman da suka ji labarin rasuwar maryamu ma. Moddibo kuwa innalillahi wa inna ilaihir raji’una yake ja kansa yana juyawa sai gani a kayi shima luuuuu ya kifa. Ai ko ana d’ago shi aka ga rai yayi halinsa. Nan kuwa koke- koke ya ‘karu shatu kuwa kuka take aljannun Na sake bugeta. Gwaggoji kuwa kasa magana tayi tana taajjabin lamarin Ubangiji ashe haka mutuwa take lokaci d’aya taji mutuwar d’anta ‘kwaya guda da rage bata dawo daga razanin ba shima mijin ya mutu, ai ji tayi ina ma ita ma ubangiji ya d’au ranta. Moddibo kam ya dace ya mutu ranar juma’a aka sadashi da gidansa Na gaskiya. Haka rayuwa take Allah yasa mu cika da imani . Gwaggoji daga ranar bata sake samun lafiya ba. sai dai a kwantar a tayar, hankalin shatu ya matu’kar tashi duk ta sake firgai firgai ko wanka batayi, bata so ta rasa gwaggoji a karo na hud’u Ta san idan ta rasa gwaggoji gatanta ya gama zubewa warwas. Mutanen nan taga basu da zumunci ko a yanzu haka ita take yiwa gwaggojin komai hatta da gyara jiki idan ta’bata. Iyakacinsu da su abinci shima ko yaro’karami zai iya cinyeshi. Ranar wata juma’a da yayi dai-dai da rasuwar malam sati takwas, suna kwance gwaggoji na nishi sans-sama tace “ shatu ko bayan raina kada ki zauna ana tunda kince maryamu ta gaya miki inda magaifiyarki take kiyi tafiyarki can, wadannan mutanen kowa kansa ya sani, ga ‘yan ubanci da suka a kansu ba zasu ri’ke ki da gaskiya ba , ina jin tsoron in mutu in barki anan don haka na dad’e da tanada miki kud’in mota.” Ta fad’a tana lalube a cikin bujenta dubu goma cif ta ciro ta mi’ka mata. “Ki’boye shatu ki adana su Allah yayiwa rayuwarki albarka ya kareki daga sharrin dukkan abin ‘ki, baki da wani gata sai dangin mahaifiyarki saboda haka ki tafi can ni na san lokaci na yayi, mutanennan mugaye ne duk ‘yan uba suke da malam dalilin gallazawar da suke mana da saran ‘boye yasa muka gudu muka barsu yaranmu ta dalilin azabarsu su uku muka rasa don haka kema ba zasu barki ba....” tari ne ya fara sar’keta tuni ta fara aman jini, zuciyar shatu ta bushe Ta riga ta saba da mutuwa ta san ita d’inma mutuwar zata yi. A Jikinta kuwa gwaggoji ta saki kalmat shahada ta mutu, ko alamar hawaye babu a idon shatu sai zuciyarta data ke wani tu’ku’kin ba’kin ciki. Ta ja mayafi ta rufe mata fuska taja gefe tana jan wani numfashi mai huci ta tabbata yanzu bata da wani gata........ Sai asuba ta sanar da mutanen gidan mutuwar gwaggoji. Ba tare da wani nuna jimami ba su kayi jana’izarta aka kaita gidanta na gaskiya. Bayan kwana bakwai rayuwa ta canjawa shatu zancen gwaggoji ya fara tabbata, ko abinci basa bata sai tayi musu aikatau. Karshe suka ce zata fara fita tallan nono bayan ga ‘ya’yansu mata basu d’ora musu ba. Cikin dare taji jatau suna shawara da d’an uwansa wai su had’a ta aure da liti yaron da kowa ya shaida d’an Ta’addane, ai kuwa shatu a daren ta mi’ke Ta hau shiri tabbas lokacin barinta garin yayi a yau zata tafi dangin uwarta. Cikin duhun daren ta fito sai dai kafin ta kai ga d’arewa’karamar katangar jatau ya hasketa. Waye nan....... [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 - 3 “Waye nan” jatau ya sake fad’a da sauri shatu ta juya tayi kamar zata shiga bayan gida, murya can ‘kasa tace “nice zan zaga ne “ tsaki yayi ya shige yana bambamin fad’an “iskancin banza da wofi kawai ki nemi frigita ni cikin tsohon dare zan yi maganinki mai kama da ifritan aljannu” shatu dai bata ce komai ba tabi bayansa da harara tana sakin ‘kananan tsaki “ aradu Allah zai kaimu lokacin da zanyi maganinku “ yana shigewa sad’af- sad’af Ta shige bayan gidan ta kuma haure’karamar katangar ta bar gidan a guje. Shatu duk da kasancewarta yarinya da ba zata gaza shekara sha biyu tana da wayo da kaifin basira, hakan yasa bata sha wuyar kai kanta tasha ba, ta hau motar da zata kaita har cikin gari sannan aka saka ta a motar garin bauchi. ************* Tafiyar awowi ce ta kaisu bauchi ko daga nan ta tambayi motar katagum, yaran tasha yasa ta a motar da zata kaita tafawa balewa daga can ne zata samu motar katagum. Suna isa kuwa kasancewar gidan babban gidane bata sha wuyar nemansa ba a kasadata da family house din nasu. Duk inda ta wuce sai an bita da kallo kasancewar tayi kama da mutanennan da ake kira bararoji, jikinta dukun-dukun hakanan kanta she looks very dirty. Sam bata damu da rufe gashin kanta ba haka take tafe wurjanjan da silifas wari da wari a ‘kafarta. Gidane babba irin ginin mutanen da , mai dauke da d’akuna birjik a kowacce shiyya, kasancewar nan ne ainahin gidan sarauta na garin, yasha gyara sosai da paint kana gani dai kasan ba wahala a tattare da ahalin gidan. Fili ne fetal ga manyan bishiyu ko ta ina. Rashin sanin inda zata yasa ta nufar wasu yara da taga suna wasan’kwallo a harabar gidan, ganinta a gurin yasa suka arce da gudu don su tabbas zatonsu aljannahce. Tsaki shatu taja had’e da komawa can gefe da ‘kullin kayanta ta zauna. Iface-Ifacen yaranne ya fito da ahalin gidan a rud’e suna duban yaran da suke fad’in “Aljannah Aljannah “ shatu ta girgiza kai tana juyosu daga waje a zuciyarta tace “ai kuwa sai kunci ‘kwal uwarku akan iyayenku zan huce a aljannar zan zo musu kafin na bayyana kaina “ da sauri ta hargitse sumar kanta tsaf ta mi’ke ta hau zare ido ta shagid’e hannu d’aya, Ta dumfari babbar shiyyar da taga yaran sun nufa. Ba zato ba tsammani suka ganta a tsakiyar filin kan kace meye iyayen yara sunyi hanyar neman tsira sai tsohuwa dada da aka bari jikinta yana’bari tana fad’in innahu min sulaimanu kuyi min aikin gafara wallahi ba laifina “ shatu ta cusgune fuska ta dumfari dada ai kafin kace mai dada ta saki gudawa da fitsari a wando ganin tana shirin fad’uwa shatu ta tintsire da dariya “ ke tsohuwa dakata kada ki sume min ni ba aljannah bace kamar yarda kuka d’auka mutum ce ni d’iyar maryama ‘ya wajen d’anki Lamid’o “. Dada ta zaro ido tana kallonta kafin tace “ki rantse da Allah “ shatu taja tsaki “ kwarankwatsa ni ba aljannah bace ko kinga kofato a ‘kafata “ sai sannan dada taja dogon numfashi tana zamewa a jikin bango zata zauna. Shatu ta kalli gudawar tace tana toshe hanci. Sai sannan dada ta lura ta saka salati da sauri ta rarrafa tashiga bayan gida shatu kuwa sai tuntsira dariya take. Sai dada ta kimtsa ta dubeta bayan ta kaita rumfarta taje ta kira matan gidan “ to duk ku fito ku ji min bayani wai wannan d’iyar maryama ce maryaman da tuni lamid’o ya sallamata ga d’iyarta mai kama da jinnu ta bayyana “ shatu ta girgiza kai a hankali ta furta “zaki bayanin wannan ma “. Sai sannan kowa ya fito cikin tsananin ta’ajjibi ana kallon shatu wai wannan jinin lamid’o ce yarinya kamar fulanin daji ita kuwa maryama mai yayi mata zafi ta za’bi rayuwar daji akan rayuwarta cikin gata da mutuncinta “. ‘Daya daga cikin matan ta fad’a shatu ta watsa mata wani kallo had’e da cewa “ yo haka ‘kaddarar Allah ta za’ba mata kuma kada a sake a zagi uwata don kuwa bata raye aradu raine zai ‘baci “ Ta fad’a cikin karyayyiyar hausarta ta fulanin usli. Gaba d’aya suka zaro ido dada ta saka kuka “yanzu’yar nan kika ce maryama ta mutu? Innalillahi yau ya lamid’o da liman zasuji da wannan ba’kin labarin kullum zancen su na maryama ne “ Ta fad’a tana jan majina hawaye sha’be-sha’be, kafin ta share hawayenta tsaf ta mayar da kallonta kan shatu tana mata kallon ‘kurilla “ wace shaida zaki bamu mu yarda ke d’in jininmu ce d’iyar maryama daso?” Shatu ta mata wani kallon she’ke’ke aradun Allah babu shaidar da zan baku sai na cika cikina tunda ku kam baku san zuru ba kun san wahalar da na hya kafin nazo nan amma ba wanda yace min ga ko ruwa Na hya “ dada tace “kwarai da gaskiyarki ke harira kawo mata abinci ke kuma furera ki kira matar lamid’o kice ko mai suke su biyo jirgi daga habuja suzo hukuncin ubangiji ya tabbata.” Ana kawo mata abincin ta fara ci hannu baka hannu kwarya dad’in abincin har tsakar kanta ga nama zu’ku-zuku wanda rabonta da cin nama tun sallahr layya ta bara idan har bata manta ba. Taci tayi nak ta sha zo’bo sai sannan ta fara washe baki tana dariya ta kalli dada “to ko ki yarda ko kada ki yarda ni d’in diyar maryama ce ga hotunan da ta bani kafin rai yayi halinsa” ta fad’a tana zaro hotunan daga bujen da yake jikinta. Wanda suka san maryama da wanda sai a hoto suka santa duk suka zaro ido dada girgiza kai “ ba shakka hukumullahi la ajabun innalillahi wa inna ilaihirrajiuna wato maryama daso sallama tayi damu “ hawaye shabe shabe dada ta saki tana sake rushewa da kuka , sai kuma ta dubi shatu tana fyace majina “ ikon Allah wato shi ubannaki bararo ne?” Shatu ta zaro ido “ kan bala’i inji uban wa?” Ta fad’a tana cizon yatsa [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -4 ELEGANT ONLINE WRITERS**** Dada ta zuba mata idanun tsofaffinta , cikin gatse tace “inji ubanki muji da ya sace mana’ya ya gudu da ita” shatu ta girgiza kai had’e da mi’kewa a katifa tayi kwanciyarta. Ba a d’au dogon lokaci ba barci yayi awon gaba da ita. Dada ta bita da harara “ wannan yarinyar daga gani ‘yar daru ce bari kakannin naki suzo ni za’a barwa ke sai na koya miki hankali tukun, ke fure kira min su lamid’on kiji sun taho “ furere ta amsa daya bayan d’aya suna ficewa daga d’akin. Koda furere ta kira wayar taji shiru ta tabbatar sun taho kenan tunda ta san ba sajin kud’in jirgi kullum a tafe suke. Dada tana zaune tana lazimi ita kuwa shatu barci takeyi sosai abinta cikin kwanciyar hankali. Liman na dawowa dada ta sake bashi labari, cikin farin ciki yake kallon shatu da ba abinda ta d’auko na uwarta da alama can dangin ubanta ta d’auko don ban ga kamanni ba “ ya fada yana kallon dada, dada ta ta’be baki “ yo kaima dai ka fad’a yarinya kamar bararo ko fulanin daji anyi magana tace inji ubanwa? Bari su su lamid’on suzo sa tantance idan jininsu ce ko Ba tasu ba sa san yarda zasuyi da ita, ni wallahi tulin sumar kanta ne ma da idanunta suke ban tsoro yarinya kamar d’iyar jinnu don kyau “. Malami dariyar su ta manya kawai yayi gani n shatu ta mi’ke ba tare da sanin dadar ba tana ta harararta “ yo ki fito kice min kawai baki yarda dani ba mana Allah na tuba na me zan zauna ina muku’karya “ Sallamar su lamid’o ce yasa dada yin shiru bata tanka ta bata Allah ya sani tsoro yarinyar ke bata “ maraba lale da iyayen maryama kuzo yau dai kuga jikarku d’iyar maryama “ da sauri suka ‘karasa d’akin suna watsa idonsa akanta ta kuwa ‘kuri tana kallonsu.maman maryama tace “dada kada kice min wannan jinin maryama ce?” Dada ta ta’be baki “babu wai itace maryama ta haifo muku bararoji mai kama da ubanta. Ai mama bata’karasa jin abinda zata ceba ta ‘karasa da sauri ta kamata ta rungume “ Alhamdulillah ashe zan sake ganin maryama?” Shatu ta zame jikinta “ ai kuwa ba zaki sake ganin maryama idan dai ba yau kema zaki bita yarda ta tafi ba ashe kuna sonta ku ka kasa bata burin ranta akan haka ta gudu ta bar gida ta bar gatanta ta gwammace rayuwa cikin daji “. Lamid’o zama yayi yana kallon yarinyar mai cike da tsiwa da surutu mama kuwa sake janta jikinta tayi “ mun dade muna neman inda zamu ga maryama sai yau Allah ya nufa “ cewar lamido dada ta girgiza kai “ yau ai kaga dalilin da yasa ba zaku ga maryama ba tana can ‘kungurmin dajin da ba wuta balle a samu tv ta ina zata ji cigiyarta da ake ba’kin cikina d’aya ne Allah ya dauke maryama ba tare da mun sake ganawa ba sai bararon ‘yarta da ta bar mana” dada ta fad’a tana fashewa da kuka, mama ma zama tayi da’bas a kujera tana juya maganar dada lamid’on kuwa salati kawai yake ja , yanzu maryama ta mutu maryaman da ya dad’e yana nema ya nuna mata gata dama tuni ya yafe mata , mama kuka ta saka sosai tana rungume shatu a cinyarta cikin tsananin’kaunarta sam bata damu da daud’ar da take jikinta ba. Shatu taji zuciyarta ta karye da tausayin kakanninta mutuwar innaji ta dawo mata sabuwa kar itama ta rungume mama tana sake sakin kuka mai ratsa zuciya mama ta sake rungumeta tana shafa himilin gashinta. Tsawon lokaci suna cikin jimami kafin lamid’o ya kalli shatu yace ya sunanki?” Murya a dashe tace “ shatu “ lamid’o ya jinjina kai “ to ya akayi kika gane nan kika zo ina so naji labarinki da garin da kuka zauna da labarin rayuwar maryama a garin....... shatu ta gyara zama daidai lokacin da wani daddad’an’kamshi ya ziryaci hancinta tana d’aga ido ta hango mai sallamar da sauri ta mi’ke tana wara ido tana fad’in “innaji “ mama ta kama hannunta “ zauna aysha ba mamanki bace yayarta ce da take bi ana ce mata mammah “ mammah da take tsaye ta waro ido tace “ mama kada kice min y’ar maryama ce ina maryaman ina ‘yar uwata alhamdulillah yau burina ya cika “. Mama hawaye ya ziraro mata don Ta san za’ayi haka Ta sani sarai deejah bata da buri irin taga maryama kullum zancenta kenan. Shigowar samarin yaran deejan yayi daidai da lokacin da mama tace “ Addu’a ‘yar uwarki take bu’kata yanzu Allah yayi mata rasuwa wannan y’arta ce Aysha da ta bari “. Gani su kayi mammah kawai ta zube numfashinta na ‘kokarin d’aukewa da sauri y’ay’anta su kayi kanta suna jijjigata had’e da kiran sunanta amma shiru. Dada ce ta d’ebo ruwa ta watsa mata sai kuwa ta kawo ajiyar zuciya “mama don Allah kice min wasa kike ko mafarki nake ba maryama ta bace ta mutu “ Lamid’o ya mi’kar da ita zaune Kafin yace “ Allahn da ya fi mu son maryama ya amsheta addua tafi bu’kata yanzu sai kuma d’iyarta da ya bar mana mu dinga kallo muna jin dad’i Alhamdulillah da wannan hikima ta ubangjji “. Da sauri mammah taja shatu jikinta ba tare da ‘kyankyaminta ta rungumta tana bata sumba a gefen kumatu cikin nuna mata tsananin ‘kauna take share mata hawaye tana kallonta with so much caring , saurayin d’anta da yake gefe imran ya hau ‘bata fuska cikin tsananin mamakin mammahn da bata’kyankyamin wannan yarinyar da Daud’a ta samu wajen zama a jikinta. Zuciyarsa har tashi ta fara yi saboda mutum ne shi mai tsananin’kyankyami da tsafta har da ta siyarwa. Runtse idonsa yayi kawai ba ya ma son sake kallon wannan kwamacalar. Ya bud’e kujerarsa wata karama da ya shigo da ita daga motarsa ya zauna. Sai a lokacin dada ta kula dashi duk da’kamshinsa ya sanar da duk ahalin gidan zuwansa’kamshin turarensa na amouage interlude 53 ya karad’e gidan sanye yake cikin black jeans da white long sleeve shirt ta Ralph lauren polo ya gyara glass dinsa da yayiwa idonsa kyau ba’a ganin ‘kwayar idonsa gashin kansa a kwance luf, murya a dashe yake gaida lamid’o da dada. Dada cikin mamakin halinsa na ko da yaushe tace” jakadan turawa yaushe ka bayyana a ‘kasar.” Cije lips dinsa yayi bai bata amsa ba sai ammar kaninsa ne yace “ yau kwanansa biyu “ dada ta kyabe fuska “ ai dama shi ba zaka ganshi ba Sai a dangin uwarsa saboda sun fimu farcen susa ammar kaine namu Allah yayi maka albarka yo wannan dama fuska kamar hadarin kaji wake maraba dashi ga shegen tsurfar tsaftar tsiya da ‘kakale aikin banza ko mu har a gaya mana tsafta “ . Ammar dariya kawai yake shi kuwa imran ya’kare tsuke fuska shi yasa sam baya son zuwa gurin tsohuwar nan mai shegiyar maganar tsiya. Lamid’o ya gyara murya kafin ya dubi Aysha “ ina jinki ayshatu bamu labarin “ ai kuwa ta sake gyara zama ta jingina kanta a jikin mommah ganinta take kamar innaji wallahi. Mommahn ta kara janta jikinta duk da warin da bakinta da jikinta yake bata’kayamaceta ba tana sauraran yarda take basu labari tiryan-tiryan. Kafin ta gama bada labarin gaba d’aya gurin kowa kuka yake har ammar banda imran da ya d’auke kai gaba d’aya haushin yarinyar yake ji ga shegen surutu kamar kanya ba mamaki ma ‘karya take ba jininsu bace idan banda haka mai ya had’a su da bararoji. Yanzu haka had’a baki a kayi da ita tazo ta cucesu mutanen duniya da basu da gaskiya musamman su d’in da an sansu a gari . “ ya kamata ku bincika kafin ku tabbatar da gaskiyarta “ hakan kawai yace yaja baki yayi shiru kamar bashi yayi magana. Momma ta d’ago a fusace zata yi magana lamid’o ya d’aga mata hannu ita kuwa shatu wata harara ta zuba masa da ya sashi ware ido yana kallonta cikin mamakin rainin da ta nuna masa sai kuma yayi Kwafa. Dada ta gyara zama “ yo saboda Allah ai gaskiya bature ya fad’a nima fa mamaki nakeyi ace wannan bararojin jininmu ce to ka fad’a ace ina ka fito don dai mune masu kalan dangi sai kuma mu had’a jini da bararo “ mommah idan ranta yayi dubu ya ‘baci ta kalli dadan kafin taja’kafar shatu ta nunawa dadar “ duk wanda ya san yar uwata maryama ya san wannan copyn kafarta ne da hannunta dada ki daina daka ta imran da shegen halinsa dinnan na bin kwakwkwafi a ina yasan maryama balle ya tantance jininta maryama da ta bar gida yana shekara guda duk’kaunar da maryama ta nuna maka ban mance da ita ba.” Imran ya ta’be baki kawai ita kuwa shatu zaro hotuna tayi ta mikawa mommah da takardar da innaji ta bata tace ta basu. Mommah na gani ta mikawa lamid’o “ Baba kalla kaga wallahi rubutun maryama ne wannan tabbas “ lamid’o ya kar’ba ya kuma shaida tabbas rubutun d’iyarsa ne. Sun ci sun sha akayiwa maryama addua sannan su lamid’o mazauna abuja suka fara haramar tafiya. Mama tace shatu tayi wanka ta canja kaya kafin su wuce shatu ta had’e rai sam bata san zancen wanka. Mommah ce tace” haba mama na zata zaki bar min ita mu koma kano tare musamman ganin bani da y’a mace ashe maryama ce zata haifa min” mama ta girgiza kai imran yana zaune a gefe yana adduar kada Allah yasa mama ta amine banda rigimar mommah ya zata kai musu bararo gida......😂😂😂😂 To fa! [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 ELEGANT ONLINE WRITERS...... -5.... Momma ta sake gyara murya cikin kwantar da kai ta furta “ Don Allah mama ki bar min ita kinga ke kina da wasu y’an matan ga hafsa ga nahnah ni kuwa Allah bai bani haihuwar d’iya mace haihuwar ma daga ‘ya’ya biyun ba saketa nayi ba.” Mama ta girgiza kai “ Gaskiyar magana addarsu ba zan iya ba su wadancan da kike magana ina na gansu kun kwashe kun kai can uwa duniyar turkey karatu, yanzu kuwa ita zan dinga gani kamar maryama da na rasa “. Dada taja tsaki “ kaji min wani zancen shirme Idan da wanda ya dace ya ri’ke wannan ‘ya ai dijama ce yo fisabilillahi tana da wata uwar ne bayan ita a duniya ai itace take da iko da yarinyar nan ba ke ba daga kawai kin haifi uwarta, don haka na zartar da hukunci dijama ki tafi da ita ke kad’ai zaki iya da wannan bararojin mai ido a tsakar ka ko samarinki sa ladabtar da ita musamman wancan miskilin kafi mahaukaci ban haushi da idanunsa kad’ai sun isa hukunta ‘yar banza idan ta’kamarta ido ai gidan ta tarar.” Wani kallo shatu ta watsa mata a zuciyarta tace “ sai nayi maganin wannan tsohuwar kafin ta sheka barzahu “. Liman da lamid’o murmushi kawai suke ganin yarda mama ta had’a rai alamar sam hukuncin dada baiyi mata ba sai dai ba yarda za tayi da ita. Momma kuwa sai murmushi take tana sake jan shatu a jikinta. Daga gefe kuwa imran ne yake ta watso mata harara kamar ya sha’keta ta mutu tabbas banda an kusa bikinsa zai bar ‘kasar da amaryarsa ‘yar abuja zubin london inji dada da barin’kasar zaiyi kafin a sake ganinsa kuwa sai an yara. Ya kalli agogo yana mi’kewa “Momma ya kamata muyi haramar komawa saboda akwai abinda dada ya sani a company ban kai ga hattamawa ba kuma kinga mota muka biyo “ Duk wannan dogon zancen yayi shine saboda baya so dada tace kwana za suyi yamma tayi. Dada ta zabga masa harara da ficificin idonta na tsoffi “ Ma’karyacin banza Ka dai ce ba zaka iya kwana anan ba saboda shegen gwalangwasonka kada kayi ubanka’karya salihin bawa dashi ko da yake shima ya zama d’an banza watansa nawa bai zo ya dubani ba ko don bani na haifo wanda ya haifi ubansa ba amma ko bakomai ai ubannasa aminin lamid’o ne, shikkenan dai Allah raka taki gona ban kuma ce Ka gaya masa ba bare kasa ya daina min aiken wata da ya saba ko bakomai ai d’an albarka ne tsiyarsa ta rashin zuriya ta bishi sahura dai taga takaici da jikanta baya son ziyara”. Gaba d’aya gurin ba wanda baiyi dariya ba har shatu idan Ka d’auke imran da ya sake kicin-kicin da fuska ya d’aureta tamau ya mayar da kud’in da yayi niyyar bawa mutanenta da ita kanta aljihu, yasa kai ya fice bayan yayiwa liman da lamid’o sallama. Dadah ta gyad’a kai “jarababbe umma ta gaida aisa gayyar na ayya ke dai dijama kin haifi ala’ka’kai.” Murmushi kawai tayi ta mi’ke tana ri’ke da hannun shatu ta furta “Allah dai ya shirya mana zuri’a bari mu wuce kada dare yayi don ma mugun gudu yake a motar “. “ wani irin gudu ki gaya masa ya tafi a hankali bana son shashanci “ lamid’o ya fada yana kallon babbar d’iyar tasa cike da kulawa ya san sosai take jin zafin rad’ad’in mutuwar nan “ kuma ki cire damuwa a ranki kada kije kiyi tunani har ciwonki ya tashi maryama addua take bu’kata yanzu, ita ta dace ko bakomai tayi mutuwar shahada tsakaninmu da ita addu’a dafatan muma mu cika da imani “ lamid’o ya sake fad’a yana kallon’yar tasa ba tare da dubi da hararar da dada take watsa masa ba “ Ba shakka zamani wato lamid’o a gabana kake lallashin ‘yarka ta fari kai Allah da ya tsinewa nasara da ya kawo boka har tayi sanadin rusa al’adarmu da dane ko inuwa d’aya ba zaka had’a da dan fari ba balle har zance ya shiga tsakaninku tur da wannan wayewa, ko da yake har gwara kai ba gani ba na tsaya ina magana da kai da iyayenan zasu dawo da sunyi tur da haihuwata kai ku tashi ku tafi kada wanda ya sake dawo min nan balle ku sake sakani rashin kunya wai da bakina nake kiran sunan lamid’o waliyazubillah duk da dai na uku ne kai amma wa ya san na farko da na biyun Allah na tuba tun kan ayi suna suka mutu ai dai kai ne dai na farkon....” gaba d’aya gurin dariya ake suka fice suna mata sallama Momma tace “ Danger number one “ Ta mudubin motar ya hango fitowarsu da sauri ya waro sexy eyes ganin da yarinyar aka fito mai hakan yake nufi wai wannan’yar dajin motarsa zata shiga kai ina impossible ai da sake. Ya fito daga motar daidai lokacin’karasowarsu mommah tace “bud’e motar mana imran, yamma fa tayi “ ya ‘bata fuska sosai “ Momma yamma fa tayi kuma gaskiya gudu zanyi sosai why not ku kwana anan idan yaso gobe nayi muku booking flight ku taho.” Momma ta watsa masa wani kallo ta san sarai nufinsa Aysha ce baya son ta shiga motar bai kuwa isa ba zata nuna masa ita ta haifeshi “ sannu ubana to yau d’in za mu tafi idan yaso’karewar gudu ka mayar da motar taka jirgi bud’e mana malam “ fuska a d’aure tamau tayi maganar tana mamakin halayen imran da sam bata san inda ya kwaso su ba. Jiki a salu’be ya bud’e motar had’e da mi’kawa Ammar key d’in “ kuje I will manage ko a hotel ne by morning insha Allah zan bi flight na taho and make sure kuna zuwa ka kira car wash su d’au motar nan every thing na cikinta ya zama clean.” Ammar ya kar’bi key had’e da bud’e driver seat momma ta waro ido tace “ yana ina shi “ Ammar yaja numfashi don yasan fad’an momma shi kuma yana son d’an uwansa baya son’bacin ransa “ Momma zai zo ya tuna akwai yana da abinda zaiyi a bauchi “. Gani yayi kawai momman ta fita ware ido tayi tana kallon imran jingine jikin bishiyar’kofar gidan kallo da take masa ne yasa shi rusinar da idanunsa baya jurewa sun saba tun suna yara da idon take hukunta su, hanya kawai ta nuna masa ta shige. Ransa a ‘bace ya bita tabbas ya san dai kafin ya isa gida wani ciwon sai ya kamashi. Shima Ammar d’in kallo d’aya tayi masa ya fito ya koma d’aya seat d’in zuciyarsa fal da tausayin d’an uwansa don ya san kam yau sai ta Allah. A salu’be ya tada motar bayan yayi adduar tafiya الحمدلله الذي سخر لنا... zuwa Karshe ya kuma ware a .c don ya kore masa warin jikinta da dum da motar tayi har da su fess turaruka. Momma tana kallonsa tana’bata rai cikin’kyamar banzar d’abi’arsa. Shatu kuwa kwafa tayi don sarai ta san ma’anarsa ta hakan wato kyamarta ma yake yi ai kuwa za tayi maganinsa kafin ta bar motar, ba mamaki ma bayan fitsari har kashi sai tayi a motar....😂😂. Wani irin gudu yake shararawa duk a tsorace suke a motar ganin yarda yake mommah kuwa ta’ki magana sai addu’a da take a zuciyarta. Shatu kwance take luf a cinyar mommah wani barci ne yake fusgarta, cikin hukuncin ubangiji kuwa cikinta ya fara murd’awa ta daddage ta saki wata tusa da ta d’umame motar gaba d’aya Allah ne ya kiyaye saura’kiris ya saki sitiyarin motar yaja wani wawan burki, ammar ya dinga’kok’arin’kinshe dariyar da ke cikinsa amma ina sai da ta bayyana a guje ya fice tuni ya fara kwara amai, Ammar ya fito masa da ruwa yana aikin jera masa sannu. Momma kuwa duk da tausayinsa ya shigeta haka ta gintse. Shatu sai dariya take yi tana’karawa momma tace “ wallahi shatu idan ya kamaki ba ruwana “ “ yo mommah ba k’yamata yake ba saura gudawa ma “ Mommah ta waro ido “ kada ki fara shatu idan ba so kike ya kashemu a titi ba kina ganin wawan burkin da ya sha Ba don Allah ya kiyaye Ba kowa a bayanmu ba da tuni mun mutu.” Shatu ta zaro ido “ momma mutuwa kuma a yanzun da zan fara jin dad’in rayuwa aradu ma ki daina wagga zance yo tunda nake ban ta’ba tunanin zan shiga wannan abin ba ban Ta’ ba ganinsa ba sai yau amalanke muke shiga garinmu da zanzo nan kuwa motar kayan miya Na shigo aradu dana shiga nan na zata aljannah nake “ mommah ta girgiza kai “To kada ki sake abinda zai zubar damu a titi motoci su take mu mutu.” Ta d’aga kai. Ya huta sosai kafin yace “ Ammar jeka Kai bud’e glasses d’in motar ventilation ya shiga ka fesa air freshners tabbas Ba mamaki mommah ta d’auko ajalina “ Ammar ya d’an shafa bayansa “ bros ba zaka mutu ba just because of her sai kwananka ya ‘kare Ka dinga daurewa pls mommah bata jin dad’i the way she looked at you ka dinga controlling temper Dinka” hannu ya d’aga masa “ jeka kayi abinda nace maka kawai ni Na san abinda zanyi muna zuwa gida I will pack everything nawa na tare “ Ammar ya zaro ido “ saura fa 4 months bikin ya zaka tare yanzu “ Imran tsaki yayi idan ban tare ba so kake na mutu ko?” Ammar ya juya yana’kunshe dariyarsa ya gama duk abinda ya sashi sannan ya dawo yana kallon yarda yake mayar da numfashi alamar ya galabaita a aman “ Bros mu tafi kada dare yayi “ mikewa kawai yayi ya mi’ka masa key d’in “ muje kayi driving I can’t do it “ Ta mudubin motar yake watsa mata harara ta saki baki sai barci take har da munshari ya sauke duk glasses d’in iska Na shiga motar a zuciyarsa yace “ Gwara a tafi haka “ momma dake kallonsa ta ta’be baki “ zan baka mamaki imran kada Ka shiga hankalinka “. Idan ba’a commnts zan dakatar da book d’innan..... [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -6 ELEGANT ONLINE WRITERS ****** Ammar cikin nutsuwa yake driving har suka isa cikin garin kano’karfe 8:00 dai-dai, shatu lokacin har fitsari ta janga’ba a kujerar ba tare da sanin mommah ba. A unguwar railway su kayi parking bakin wani tangamemen gida gari guda, da tafkeken gate, gani tayi kawai gate din ya zuge ba tare da tasan wanda ya zugeshi ba.Automatic gate ne. Ammar yayi packing a packing space. Momma ta bud’e ‘kofar had’e da jan hannun shatu a hankali ta waro ido ganin gurin da lema murya ‘kasa-k’asa tace “ shatu fitsari kika yi?” Shatu ta d’an ta’be baki “ To mommah fitsarin ne ai ya matseni kuma ina cewa zanyi zai fara masifa “. Momma tayi saurin rufe mata baki don kada imran da ya fice da sauri yaji “Muje kafin ya ankare “ da sauri shatu ta fita daga motar ammar yayi dariya yana tunanin yarda za’ayi da cakwakiyar’yar mommah da yayansa, yasan dai kwarai za’a buga show. Suna shiga tangamemen falon kamshi ya doki hancin shatu ga sanyin A.c ta lumshe ido had’e da runtse ido tana bud’ewa tabbas dai da a mafarki taga wannan gidan to tabbas zata ce aljanna tayi mafarki da ita. Momma ta ri’ke mata hannunta ta kaita’kofar wani sashe suna shiga ta kaita wani d’aki kusa da nata “ daga yau ga d’akin Ayshata muje in nuna miki komai a toilet kiyi wanka ko da yake wannan wankan na yau yafi ‘karfinki da kaina zan miki da nace ma in kaiki saloon to bana so su fara ganin wannan daud’ar kannaki jira ni anan am coming.” Da sauri ta fita daga d’akin shatu ta sake ware ido tana kallon gadon yanzu wannan d’akina ne gado na da sauri tayi tsalle a gadon tana tintsira dariya “ ahe dai ina da gata muke zaune can a dajin Allah aradu innaji ta kwari kanta cabd’i” Shigowar mommah yasa tayi shiru momma ta shige toilet ta zube kayan da yake hannunta duk mayukan wanke kaine da combs dama toilet din akwai dryer. Shatu ta fara’bata rai sam bata son a ta’ba mata kai da dai mommah zata gane da ta kyaleta. Momma ta zare du’kun’kunennan mayafin nata ta zaunar da ita bakin jaucuzi ta fara kunce tufkekken gashin kanta mommah tayi mamakin ganin tumulin gashin ta ji’kashi ta saka shampoo ta barshi for a minutes sannan ta fara had’a ruwan da zata dirje daud’ar Jikinta. Sosai ta wanke kan sai sheki yake wajen wanka ne shatu Ta fara’boye-‘boyen jiki mommah Ta harareta “ zaki tsaya ko sai na ‘bata miki rai ke da ko irgar dangi baki fara ba to koma kin fara ni ba uwarki bace “. Shatu Ta d’an sunkiyar da kai mommah Ta saki murmushi “ Ashe kina da kunya.” Tas shatu Ta fito duk da dai sai a hankali zata baje amma ko bakomai anfi baya. Fitowarta ne yasa momma ta tsaya domin ba kayan da zata bata tasa tsaki tayi tace “zauna nan ina zuwa bari na aika ammar ya siyo miki ready made kafin da safe mu shiga kasuwa “. Tana fitowa babban falo ba taga ammar ba sai imran da yake zaune yayi wanka da fara jallabiya tas a jikinta mai gajeran hannu a jikinsa yayi kyau sosai kana ganinsa kaga mutum mai mutu’kar tsafta. Sai baza’kamshin turare yake yunwa ce take cinsa ya aika ammar yayi musu take away don baiga alamar masu aikin sunyi girki ba, may be basu zata zasu dawo ba.” ina Ammar?” Momma Ta fad’a tana tsatstsare sa da ido , Imran murya can’kasa yace “ Na aike shi eatery samo abinci.” “ sai ka tashi kai na aikeka samowa Aysha kayan sawa ba tazo da kaya ba “ ta fad’a tana juyawa ba tare da Ta lura da waro idon da yayi ba yana ji kamar ya rusa ihu ganin zata shige yace “ kud’in fa?” Ba tare da Ta juyo ba tace “ ka siya da naka “ dunkule hannu yayi ya daki d’aya cikin d’aya kamar ya tashi sama kuma ya juya da sauri ya fice daga cikin gida. Da yaje ma rasa mai zai d’auka yayi ya d’auko mata riga da wando Na maza kawai bayan ya kintata tsahonta yaga ba zata zarta hakan ba. yunwa yake ji sosai amma mommah Ta sashi zuwa siyawa wannan bararojin kaya. A falo ya ajiye kayan ya nunawa Ammar “ mikawa mommah “ ya zauna a dinning ya fara cin abincin” mintuna kad’an mommah da ‘yarta suka fito Ta saka riga da wando duk da Na maza ne sai sukayi mata kyau, mommah Ta gyara mata kai an tsaga an raba biyu, jelar gashin Ta sauka har dantsen hannunta gashi mai yawa masha Allah sai ‘kamshi take kallo d’aya yayi mata ya d’auke kai ya cigaba da cin abincinsa momma taja kujera tace “zauna “ Ta zauna tana hararar naman da yake ci tsoronta Allah kada ya cinye naman hakan yasa ta shiga tunanin yarda zata koreshi daga wajen ta kuwa daddage ta saki attishawa sai kuwa ga majina ta biyo hancinta da sauri ya furzo abincin dake bakinsa ya mi’ke da sauri ya bar wajen. Zuciyarsa na tunzirashi yayi mata dan banzan duka kawai. Ita kuwa dariya Ta fara babbakawa “ Nagode Allah yo mommah da fa cinye naman zaiyi kaf da banyi haka ba “ mommah duk da dariyar da take cinta ta gintse tace “ baki kyauta ba kings yanzu kin hanashi cin abincin Ba kyau kada ki sake Ammar bishi da abincin d’aki”. Ammar ya mi’ke yana murmushi sosai yarinyar take burgeshi shi kam sam bata damuwa sha’aninta take zubawa. A parlornsu ya ganshi a zaune ya dafe kansa sosai tausayinsa ya kamashi ya ‘karasa da abincin yana dafa bayansa Bros sorry don Allah ga abincin momma tace a kawo maka “ zubawa plate din ido yayi yana saurin ja baya gani yake zai hango majinar a cikin abincin murya can ‘kasa yace “ ‘dauki Ka tafi dashi ba zan ci ba ta had’a Ta cinye kana tunanin yau zan iya cin wani abin ko mai na kai bakina sai na tuna ‘kazamar yarinyar nan bitch “ ya mi’ke ya shige bed room direct toilet ya shige ya sakarwa kansa shower.so yake yaji zuciyarsa Ta daina’kuna. Yana dawo da abincin mommah Ta kalleshi “ baya ci ne?” Ammar a sanyaye ya d’aga kai yaja kunnen shatu dake zaune “ if you try it again Allah sai Na zaneki mommah kija mata kunne “. Narai narai tayi da idonta “ To ni ina ruwa na kawai atishawace fa tazo ya zanyi da ita to “ “ Excusing kanki za kiyi ki fita kiyi haka ake yi wai ke baki da manner ne?” Kuka Ta saka “ Ni ka daina min wannan maganar ban iyata ba idan bakwa san zama na kuma kawai kuce na tafi. Ya bud’e baki zai yi magana mommah tace “ Ammar ya isa ai da gaskiyarta to ya zatayi da atishawa fisabilillahi ni fa kada wanda ya ‘kara takura mata duk wanda Ba zai iya zama ba shi ya bar gidan. Ammar ya bud’e ido “Mommah......” “kada kace komai “ ita kuwa shatu plates d’in imran taja ta fara cin naman cewa takeyi “ Yo ai yayiwa kansa ni kuwa gaba Ta kaini......” Ammar murmushi yayi ya wuce yana furta “ Allah ya shirya “. [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -7 ELEGANT ONLINE WRITERS.......... Momma murmushi Ta sake saki ganin yarda shatu take cin abincin hannu baka hannu kwarya “ ci a hankali Aysha ba inda abincin nan zaije gashi nan ma idan baki ‘koshi ba ki ‘kara saki jikinki nan d’in gidanku ne kamar yarda kowa yake ji gidan ubansa ne.” Ammar’kunshe dariyarsa yayi ganin yarda momma ta hau da yawa yasa ya koma falon ya kunna t.v . Ai kuwa shatu a zabure ta mi’ke ta isa wajen tana sid’e hannunta “ Ikon Allah yau gani ga irin akwatin kallon d’an gidan mai gari da aka kaiwa amaryrsa da ya auro a niamey, aradu wannan tayi gomanta.” Sai kuma ta fara zabura tana tsalle ganin yarda mutane ke rawa a cikin t.v d’in ta ‘karasa tana shafawa Ammar mai zaiyi idan ba dariya ba. Momma da take gefe ta dafe kai anya shatu zata gyaru ta dawo kan saiti kamar yarda take son ta ta lura’kauyancine kawai a kanta zuciyar momma ta shiga tunani. Sai kuma ta mi’ke ganin yarda ammar yake tuntsira dariya tana zuwa ta figi hannunta “ wuce muje shashasha kina zaune yana ta tuntsira miki dariya ga sabon kamu ya samu wallahi Ammar ka kiyayeni ina lura da take-takenka ta wancan ce ta fito fili shi kyamarta take kai kuwa mahaukaciya ka d’auketa to ahir ka kiyayeni “Ammar ya guntse bakinsa “ Allah ya baki ha’kuri momma amma fa wallahi dole Na samu comedy a gidan ji fa yarda take acting wallahi illiteracy d’inta yayi yawa za’a sha fama “ “ ubanka ne zai sha famar ko ni? Ina ruwanku da ita to duk zaku ci ubanku da ni kuke zancen ashe ta imran ce ta fito fili “ Ta sake kwafa suka shige part d’inta hannunta ri’ke dana shatu. Suna shiga d’aki shatu ciki ya kad’a to an ci abinda ciki bai saba ci ba da sauri Ta kalli mommah tana yamutsa fuska. Momma Ta dubeta had’e da dafa kanta “ Me ya faru ki daina fushi ki rabu da su zan yi maganinsu ai da ni suke zancen” Shatu Ta fara matse-matse “ Ni fa mommah ba zancensu ya dameni ba yo ni ina ruwa na ai gaskiya Ammar ya fad’a. “ “ Au ni na damu kenan to meye ya dameki kike had’e-had’en fuska” “ Kahi nake ji “ Momma Ta zaro ido to “ kashin kike ji kike tsaye anan, anan zakiyi min kashin?” Da sauri taja hannunta wuce muje na nuna miki inda zakiyi don ba mamaki ma baki san toilet sit d’in birni ba” da sauri shatu ta bita ji take kamar Ta saki kashin suna shiga ta hau duba inda momma ta nuna mata shatu ta waro ido “ A wannan abin fari ‘kal dahi zanyi kahin “. Momma tsaki tayi kafin ta furta “ idan ba kiyi anan ba a bakina zaki yi ?“. Ta sake le’kawa “ Ruwa ne fa a ciki aradu ba zan zauna ba inje ruwa ya zu’keni ya tafi dani “ Momma Ta dafe kai tana kallon shatun cikin takaici “ kada fa ki sake kiyi min kashi a wando ki hau ba wani ruwa da zai tafi dake duk gidan da zaki a garinnan yawancin irin wannan d’inne sai dai idan kin daina kashin” “ To zan hau amma ki tsaya ni” “ In tsaya ki ki cika min ciki da warin kashi to ba dani ba ki hau in kin gama wannan zaki ciro kina danna nan ruwa zai zo kiyi tsarki shi kuma kashin ba barinsa zakiyi ba ki danna nan ruwa zai tafi dashi kin jini ai da kyau?” Shatu Ta d’aga tana d’ofana akan seat toilet din ta zauna. Momma ta saki ajiyar zuciya Ta ja mata ‘kofa ta fita zuwa nata d’akin a gaijye take tubus banda soyayyarta da maryama ba abinda zai kaita d’aukar shatu musamman ita da mijinta da suka tsarawa kansu rayuwar turai basa son hayaniya sam shi yasa sam basu damu da haihuwa ba sai gashi ta d’auko shatu wanda Ta san sai tayi bore kafin mijinta ya amince da zaman shatu a gidan. D’akinta ta shiga wanka kawai take bu’kata da nutsuwa. Shatu anyi abin kai bayan ta gama tayi tsarkin ta mi’ke sannan ta danna inda akace zata kore kashin idan ta gama ai ko sai tayi tsalle ta koma can gefe tana kallon ruwan abin kuma sai ya bata dariya ta sake dannawa haka tayi- tayi kafin ta gaji ta fito a zuciyarta take fad’in “ wato hi kahin ma wani matsayi ne dashi na musamman a Gidannan cabd’i Allah ya kyauta “. Ganin momma bata d’akin Yasa ta fita tana bilayin nemanta . Ganin bata ganta ba a d’imauce Ta fara’kwala mata kira duk gidan yana amsa kuwwar muryarta. Da sauri d’aukacin mutanen gidan har su Imran suka fito tunanin ko ba lafiya ba, abinka da ba’a saba hayaniya a gidan ba, dai- dai lokacin mai gidan shima ya bud’e ‘kofar part d’insa ya fito don bai dad’e da dawowa ba yaji tashin muryarta. Da kallo ya bisu ganin sunyi cirko-cirko suna kallonta. Had’e fuska tayi tana binsu Da kallo “ To wai lafiya naga kun saka ni tsakiya sai wani kallo na kuke.” Imran tsaki yayi ya juya ya shige part d’insu da ya san ma itace ba zai fito ba to barcin gajiya ya fara fisgarsa ya jiyo hayaniyarta kai mommah ta d’ebo musu damuwa.Ammar da ya lura da Dahdansu yayi saurin cewa “ welcome dahdah “ girgiza masa kai yayi fuska a had’e yace “ who is she?” Ammar ya mayar da kallonsa kan shatu da take fad’in “ Wannan sa ido da yawa yake uwa ta fa na kira baku ba” Ammar yayi saurin katseta “ ke are you mad kin san da wa kike magana “ “ kai ka san mai kace inace mad d’in d’an garinku sai kayi tayi min yaren birni so nawa zance maka bana so “ Ta fad’a tana ta’be baki . Cikin tsawa Babannasa yace “Ammar am asking you who is she I said?” Mommah ce Ta fito daga’bangarenta turus tayi ganin taron jama’ar gidan Ta mayar da idonta kan dahda “ Ai ban san ka shigo ba ina wanka.” Fuska a had’e yace “ Yayi kyau kai kuma amsa min tambayata wace shashashace wannan?” Mommah ta had’e fuska “ diyar tawa ce shashasha to ko baka santa ba ai bai kamata daga ganin ba’ko ka kira shi da shashasha ba er maryam ce sister ta wani abu ne?” Wani kallo ya bita dashi sai kuma ya hau step d’in da zai kaishi ‘bangarensa.” Almasifatu shi kuma wannan d’in waye da naga duk kun firgita da ganinsa “. Momma ta waro ido Allah ya taimaka ya shige bai ji ta ba Ammar ya watsa mata wani kallo “ ke ubannamu kike kira Almasifatu?” Cikin ‘ki’k’kifta ido tace “ Aradu ban san ubanka bane yo ai da ba zan kira shi da haka ba.” “ zagi na kika yi kenan ?” Cikin kufula Ammar ya fad’a. Momma Ta dafe kanta had’e da jan hannunsa “ Bafa zagin ka tayi ba Ammar sai kunyi ha’kuri da ita kafin ta goge” Ammar ya kad’a kai “ki daina bin bayanta fa mommah cewa fa tayi ubannaka?” “ To kayi hakuri mana haba su a garinsu ai ba zagi bane hakan “. Shigewa part d’insu kawai yayi yana nanata kalmar AlMASIFATU. Momma ranta had’e tace “ Maza wuce d’akinki kada Na sake ganin’kafarki a waje sai da safe nan gidan bama hayaniya mai gidan duka yake “ sum sum ta wuce . Momma Ta dubi masu aikinta biyu da suke kwana su kansu a ‘boye suke saboda mai gidan ya sha fad’a mata baya san shirgi, ‘ya’yansa kad’ai sun isheshi “ ku kuma mai kuke yi anan? Yawon d’aukar news ko?” Da sauri suka fice ita kuma Ta shige ciki sam bata san yau zai dawo ba ba abinda Ta tanadar masa. Kitchen d’in da yake part d’insa Ta shiga saboda tsantsaninsa komansa anan yake ita take masa komai bai yarda kowa yayi masa ba. don haka ma yayi kitchen a part d’insa saboda kar ma wata rana tayi gigin saka masu aiki yi masa wani abin. To ashe dai imran a can ya gado tsafta. Sai da ta d’ora abincin sannan ta’karasa bed room d’insa . A zaune ta ganshi da news paper a hannunsa sallamar ma ciki-ciki ya amsa ba tare da ya d’ago ba “ Yalla’bai barka da dawowa ina ta magana kayi shiru wai me ya faru ne?” Ya d’ago fuska a cusgune “ Da izinin wa kika d’auko bagidajiyat yarinyar can to bari kiji in gaya miki I can’t tolerate this nonsense maza-maza gobe ki mayar da ita inda kika d’aukota ai kin san sarai bana son hayaniya yaran ‘yan uwana ma ban yarda na ri’ke ba balle wannan yaran da bata da respect don haka ki mayar da ita, saboda bana son haihuwa da yawa Na ‘ki ‘kara aure so ba wani abu da zai sani ri’keta...........” [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -8 ELEGANT ONLINE WRITERS......... Momma tagumi ta zuba tana kallon dahda “ Amma ka bari kaji er waye kafin ka fara fad’ar ba zaka ri’keta ba, er fa maryama ce maryama jinina da muka taso tare maryaman da na sha mama na bar mata, duk ba ma wannan ba bata raye wa kake so ya rike mata er ta wa take dashi idan bani ba.” Jikin dahda ne yayi sanyi “ maryama ta mutu?” Ya fad’a cikin taushin murya ba kamar yarda ya d’au zafi ba, innalillahi wa inna ilaihirrajiuna, momma ta ja ajiyar zuciya kafin tace “ maryama ta mutu nima d’azu kira ya ruskeni daga katagum muka tafi a can muka samu ita wannan er tazo ita kuma take sanar damu mahaifiyrta ta mutu.” Allah ya gafarta mata Allah yasa ta huta amma ina mahaifinta?” Momma gyara zama cikin kasa da murya tace” shima Allah yayi masa rasuwa “ Tausayin shatu sosai ya kama Alhaji, ya Hau girgiza kai yana jaddada lamarin girman ubangiji “ Allah ya gafarta musu Allah kuma ya bamu ikon sauke nauyin ri’kon maraya “. Farin ciki ya ratsa zuciyar mommah sai sannan hankalinta ya kwanta da har ya amsa zai ri’keta “ Nagode dear bari na kawo maka abincin” . Ta fara zuba masa abincin ya dubeta “ kiyi ‘ko’kari sosai akan yarinyar nan ki koya mata tsafta uwa uba tarbiyya don sosai na lura bata da manner, insha Allah nima I will try my best naga na kula da lamarinta don kamar nauyinta ne Allah ya d’ora mana.” Insha Allah mommah kawai take fad’a zuciyarta cike da farin ciki a take a wajen ya tura mata kud’i a account ya umarceta da kashegari aje ayiwa shatu siyayya. Godiya ta sake masa ta mi’ke don fita shirin barci. ******** kwananta biyar da zuwa gidan amma har ta fara murjewa, jikinta yayi kyau masha Allah duk da haskenta bai fito gaba d’aya ba . Duk wani abin da bata sani ba mommah ta koyar da ita yarda za tayi amfani dashi a gidan.Ta fara kuma ‘ko’karin ganin ta daina rashin kunya duk da har zuwa lokacin da yarinta a tattare da ita. Abubuwa da dama bata iya cinsu har a lokacin da zarar taci sai tayi aman su saboda rashin sabo sai dai son cin nama shan madara da milo kuwa har dana maza da kauri sosai take damawa ta shanye.Ammar tuni ya fara sakin jikinsa da ita kasancewar yanzu duk ta d’an zubar da rashin kunyar an samo mata malami da zai dinga koyar da ita.Imran ne baya shiga shirginta . Yauma da wuri ta tashi, tayi saurin yin wanka da brush don kar mommah tayi mata fad’a gashi ne dai bata taje shi ba bata son gyaransa sam bata’ki kuma mommahn Ta aske shi ba kamar yarda tace. Ganin su mommah tayi suna ta aiki a gidan ta fara tunanin ko mai zai faru ake ta wannan aikin Ta kuma lura zuciyar momma sam ba dad’i don komai a sanyaye take yinsa. Momma ta dubeta tana amsa gaisuwar da take mata cikin nutsuwa” yauwa my baby kin yi wanka maza kije kiyi break fast kizo d’aki ina son ganinki “. Amsawa tayi da sauri tana isa kan dinning , Tayi turus ganin imran a dinning d’in yana break idanunsa ya zuba mata, da sauri ta dur’kusa tana gaisheshi imran ya had’e fuska. “ ke bar nan wajen before I slap you “ kallon ‘kasa-‘kasa tayi masa “ To ba yunwa nake ji ba zaka ce na bar nan.” Harara ya watsa mata sai kuma ya cigaba da abinda yake kafin bakinsa ya furta “ Dirty Girl “ zama tayi ba tare da san abinda yace “ kin san mai nace miki?”kamar doluwa ta hau girgiza kai “ ‘kazama nace miki Alhamdulillah na kusa barin gidan sai kuci’kazantarku ku kad’ai “. Ba tayi masa magana illa kallon plate d’insa da tayi yana shirin kai tsokar nama ta miyar turmeric baki ta saki murmushi kafin tace “ Ga kanan’kazami kana cin miya kamar gudawa.....” Ai da sauri ya furzar da naman bakinsa yayi wajen sink shatu ta tuntsire da dariya a hankali ta furta “ ba’kin mugu in dai ina gidannan ka daina ci ka ‘koshi “ sosai ya kuskure bakinsa ya bita da wani kallo kafin ya wuce shatu ta ja plate taci abinci tayi nak “ Allah gaba ta kaini ba gashima har nayi’kiba ba gobe ma ka sake ce min’kazama Allah mhmmn sai kuma ta girgiza kai.” Da kyar take nishi sai kuma ta tuna kiran da momma take mata da sauri ta shige sashen mommah a zaune ta ganta ta rakfa tagumi idonta har ja yayi. Jikinta a sanyaye ta ‘karasa ta zauna daf da ita “ Momma mai ya sameki?” Momma ta shafa kanta “ bakomai shatu anjima za’ayi ba’ki babar mai gidan nan zata zo don Allah don’t make any thing da za’a tafi dake a baki bana son kiyi rashin kunya ko wani abu kinji ki daina yawan fitowa kiyi tasa catoon a d’akin ki.” Shatu ta d’aga kai “ Tana da fad’a ne Mommah?” Shatu tace tana kallon ta , mommah ta girgiza kai “ Ba fad’a kad’ai ba zata iya sa daga ni har ke mai gidan nan ya koremu “ “ cabd’i muje ina duk wannan naman mu barhi “ Momma tayi tsaki “ ke kike ta nama Aysha Idan nama ne duk mai sau’ki ne gidanmu ma akwai ina son mijina bana son ta raba ni dashi “ “ Au to hi dahdan sai ya rabu dake “ momma ta d’aka mata duka “ sau nawa na hanaki cewa hi da he a maganarki ? Ba abinda zaki fahimta yanzu sai nan gaba zaki san and wacece hajja tashi kije Na gaya miki ba ruwanki da kowa, kuma ki dinga dur’kusawa har ‘kasa kina gaisuwa kin ji?” Shatu ta girgiza kai kawai daidai lokacin da suka ji dirin motoci a harabar gidan. Da sauri mommah ta mi’ke cikin rawar jiki ta fice, shatu ta bita da kallo kafin ta fita taga wacece wannan da mommah bata son’bacin ranta. Babban falon ta fita duk mutanen gidan suna zaune gefe d’aya mommah ce dur’kushe tana gaida hajja murya a cunkushe hajjan take amsawa tana yatsine fuska. Ganin yarda su imran suka gurfana suna gaisheta yasa ita ma shatu ta’karasa ta dur’kusa tana gaishe su. Hajja ta zuba mata manyan idonta “ ita kuma wannan daga ina? Sabuwar mai aiki kuka yi da har kuma ta sake ta za’ke take shiga cikin ahalin gida, Ba shakka to mi’ke daga nan kafin Na kai miki mangari.” Shatu ta d’ago ido zata aikata halinnata sai kuma suka had’a ido da mommah sum sum ta mi’ke ta shige “ ina magana an min banza ga a tsohuwar banza ko nace wacece wannan deejah?” Murya can ‘kasa mommah tace “ d’iyar maryama ce’kanwata to ta rasu shine na d’aukota “. “ shine aka ajiyeta ba tare da izini na ba ko? Ni da gidan d’ana ga a baitil mali an samu wacece ma maryama a zuri’arku?” Momma ta sake sunkuyar da kai “ ‘kanwata data bar gida da dadewa “. Hajja salati tasa “ kice min’kanwarki da ta tafi karuwanci shine kika d’auko shegiyar’yarta kika cud’anya cikin tsaftatacciyar zuri’ata, zuriar da aka Haifa ta sunnar manzon Allah to kuwa ba zai yiwu ba kai imran kira min ubanka a waya.” Gaba d’aya suja juya jin takun tafiyar dahda murya a cunkushe ya shigo, shatu da take ra’be a ‘kofa ta shige d’aki wai yau ita ake kira da shegiya ai kuwa tayi al’kawarin sai ta sa matar nan kuka. Dahda ya dur’kusa a gefenta. Fuskarsa yana d’an sakin murmushi yace “ Hajja ashe kin shigo ? Barka da zuwa ta amsa tana girgiza’kafa “ kai ka bawa shegiya lasisin zama a gidanka ?” Cikin rashin fahimtar zancennata yace “ wacece shegiya?” Kwafa tayi “ baka santa ba kenan d’iyar gantalalliyar’kanwarta maryam da ta bar gida saboda ubanta ya za’ba mata miji ta gwammace ta tafi yawan dadiro.” “ Hajja wanda ya mutu fa ya mutu mai yasa zaki dinga’bata mata gawa ba kuma yawon dadiro ta tafi aure tayi ta haifi er ta don haka wannan zancen don Allah ki daina fad’arsa “. Dada ya fad’a fuskarsa a had’e. Hajja ta sake tsuke fuska “ Ba shakka ubana to ai sai ka bari sai na zama sokuwar uwa sannan in dinga bari kana fad’a ina fad’a shashasha kawai wanda mace ta riga ta gama dashi shi yasa wannan karan da shiri na nazo kaga can to matarka ce ni na bada sadaki aka auro maka ita tunda na bika na bika ka’ki amincewa da auren shi yasa ni na auro maka ita kuma wallahi kace baka amince ba sai dai ka sake wata uwar.” Mommah wani fad’uwar gaba ne ya sameta ganin wacce aka nuna aka ce kishiyarta ce y’ar’kanwar hajjance uwa d’aya uba d’aya da ta dad’e tana zawarci kuma y’arta imran zai aura sannan ace itace kishiyarta tabbas akwai ‘kura. Dahda cikin ‘bacin rai yake kallon ta tana zaune fuskarta sai murumushi take tana rausayar da kai. Dahda mi’kewa yayi kawai yayi hanyar fita. Hajja ta sake tunzira “ Ba shakka sallamamme ai ban gama magana ba kake shirin fita wannan yarinyar na bada awa ashirin da hud’u t bar gidannan ‘bangaren da nake sauka anan amarya zata tare yanzu ne na san kayi aure da ka auri’yar dangi, Auren imran kuma na saka rana na da wata biyu, ba’kin ciki ya kasheki dijah dama ai na gaya miki ina tafe ga dai abin takaici kishiyarki kuma surukar d’anki sai ki had’iyi zuciya ki mutu, ku matan yanzu baku da buri irin ku mallakewa mutum d’a . Momma mi’kewa kawai tayi [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -9 ELEGANT ONLINE WRITERS........ Tana shiga d’akinta hawaye ya fara zubo mata, Tunani take sosai a zuciyarta so take ta hango laifin da takewa dangin mijinta suka tsaneta har haka, mai tayi musu? Shine abinda take tunani a zuciyarta, har ga Allah bata nufin kowa da sharri rayuwarta take free ba tare da kowa a ranta ba amma sun bi sun tsaneta. A gefen gadon ta zauna, shatu data gefe jikinta yayi sanyi ganin mommah na hawaye, taji duk duniya ta tsani waccan Almasifatun tsohuwar a hankali ta zauna jikin mommah itama ta saki nata kukayi. Momma dafa kanta kawai tayi alamar rarrashi. Daidai lokacin Ammar da Imran suka shigo d’akin jikinsu a sanyaye suka zauna kan cushion chair d’in da take gefe fuskarsu sam ba walwala musamman ammar, sam baya son abinda zai saka mahaifiyarsa a ‘bacin rai. Ammar yayi’kasa da muryarsa “ Momma kiyi hakuri komai lokacine, kuma wata rana sai labari.” Girgiza kai tayi “ Na kai ma’kura Ammar iya ha’kurin da zan iya kenan kun san iya lokacin da nake’kunsar ba’kin cikin hajja tun ranar da na kwana d’aya a gidannan duk a dalilin mahaifinku bai auri za’binta ba, kuma ba kowa bace za’bin nata sai wannan matar da sai da ta san yarda tayi yanzu ta auro masa ita, to lamarin ya isa zan tattara in tafi amma ba zan zauna ba’kin ciki ya kashe ni ba just like bani da iyaye, gidan ubanku ne ku zauna, bare shi gashi nan zasu aura masa wacce suke so, tun yaushe nake jan kunmensa ya rabu da yarinyarnan ya’ki, saboda kawai kyanta da kwalliyarsa yana rud’arta to yaje ya aureta amma ka san Allah ba hannuna a cikin lamarin aurenka, wanda dama don a gasa min ba’kin ciki aka’kir’kiresa.” Ta saki ajiyar zuciya bayan ta mi’ke ta shiga had’a kayanta, Ammar ya ri’ke akwatin “ please mommah kada kiyi abinda baki ta’ba yi ba da yarintarki balle da girmanki please ki rabu dasu,ko mu kad’ai zamu iya share miki hawaye, kuma wallahi at this point sunyi na’karshe, kaima yaya Imran don Allah kayi hakuri ka kyale musu’yarsu ko don kwanciyar hankalin Mommah “ wani kallo Imran ya zuba masa “ meye laifin shaheeda da zan rabu da ita, ko kana tunanin a bayansu take? To kullum maganar ta tana jin haushin abinda suke wa mommah.” Wani kallo momma ta wurga masa sai kuma tayi kwafa “ mhmn ba dai shaheeda bace Imran ka aureta ban hanaka ba, tunda lokacin da na hanakan ai baka ji ba, sai dai bahaushe yace wanda bai ji bari ba.... kai kuma Ammar kada ka sake masa magana idan ta nice ma barin gidan zanyi ba sai na zauna zanga kayan takaici ba .” Imran shiru yayi yana sake zabgawa Ammar harara sai kuma yayi kwafa ya fice. Mommah tabi bayansa da kallo tana masa addu’ar shiriya a zuciyarta ji take kamar ta rusa kuka gaba d’aya sun cusawa Imran soyayyar shaheeda ta ‘karfi da yaji da yaudara da komai. “ ka rabu dashi Ammar tsakaninka dashi Addu’a ya riga yayi nisa a soyayyar shaheeda ba zai ta’ba ganin aibunta ba.” Ammar ji yayi ransa ya sake’baci idan dai da shine ko da gold aka’kera shahida sai ya ha’kura aurenta balle shi dai ban da kyan fuska bai ga mai ya gani tare da shahidan ba tana tafiya kamar sillan kara,sai iyayi da kwainane. Shatu dai tana gefe tana kallon ikon Allah, takaicin Imran kuwa ya gama cikata. Har so take taga wacece wannan da ya fi sonta akan’bacin ran mahaifiyarsa. Ammar ya cigaba da bawa mommah ha’kuri ganin ta’ki ha’kura yasa ya fita wajen bayan ya danna kiran hajiya mama mahaifiyar mommah a cikin wayarsa. Basu san me yace ba sun ga dai ya dawo da sauri ya mi’kawa mommahn wayar, ya wurga masa harara don ta san’kara ya kai ta wajen hajiya maman. Tana sallama hajiya mama ta shiga fad’a tuni mommah ta sa kuka ta fara bata labari. Hajiya mama cikin zafi ta katseta “ kishiya saboda kishiya zaki bar gidanki akan ki aka fara kishiya?da girman ki da komai kike neman zubar da mutuncin ki to ahir ki kiyayeni kina shirin auren da’kanne da ‘ya’ya, nan gaba su kuma idan sunyi wa zai musu fad’a? To ki saurareni da kyau ki mayar da akwatinnan kafin ma su gani su ji dad’i gobe insha Allah’kannenki sun zo hutu daga turkey zasu zo kanon suyi miki hutu hisham ma dama yana ta son zuwa wajen mutuminsa Ammar. Ina shatu?” Momma ta mi’kawa shatu wayar “ maza ki masa hajia mama ce “. Shatu ta kar’bi wayar cikin rashin sabo ta fara gaisheta “ lafiya lau shatu ya ba’kunta? Gobe zaki ga aunties d’inki suna ta son ganinki.” Murmushi shatu kawai tayi saboda ba ‘yan hayaniyar a kanta. Hajiya mama ta sake cewa “ Ba dai matsala dai ko?” Shatu ta girgiza kai “ Bakomai mama” To masha Allah sai kin ga sa’ko “ hajiya mama ta fad’a tana kshe wayar. A hankali shatu ta mi’ka wa Ammar waya, ganin yarda jikinta yayi sanyi yasa Ammar ya shiga janta da wasa” shatun mommah’kalau kuwa yau na ganki jiki ya mutu? Ko don ki had’u da Babarki a masifa “ harararsa shatu tayi “ Ai wallahi ba tsoronta naji ba, don dai kawai mommah ta hana ne amma wallahi da tuni ta d’ebi kashinta a hannu yo Allah na tuba wannan ‘karamar alhakin, ka san Allah da ‘kauyenmu ne yau sai na saka yara sun mata kid’an Atire.” Ammar mai zaiyi banda dariya mommah kuwa bud’e ido tayi tana kallon shatu yarda take yi da baki “ To shatu ba ‘kauyenku bane kuma anan idan kayi wa wanda ya girme ka rashin kunya kulleka ake a gidan yara don haka be careful.” Ammar ya fad’a fuskarsa d’auke da alamar tsoratarwa. Shatu ta kya’be baki “ Ai in dai ba kayi a fili ba sai mutum yayi ta bayan fage yarda za ‘a gane ba.” Ammar girgiza kai kawai yayi yace “Allah ya shiryeki shatu.” “ Tashi maza kije kiyi sallah Ayshata ai Na san kina jin maganata ba zaki jawo min abin fad’a ba “.murmushi tayi tana mi’kewa dad’in yabon da momma tayi mata da sauri ta shige toilet ta bar momma da ta zuba tagumi tunani yyi mata katutu. Dahda da daddare da kansa ya shigo d’akin mommah ganin ko nemansa ba tayi ba. A zaune ya sameta kan sallaya da alama lazimi takeyi, jikinsa a sanyaye yake dubanta yana son matarsa shi kad’ai kuma ya san irin son da yake mata, ba don komai ba sai don yarda bata tsallake umarninsa kuma iya iyawarta take kyautata masa ba ta son ‘bacin ransa sam. Tana ganinsa ta d’an d’auke kai idanunta yana kawo hawaye. A gefenta ya zauna had’e da ri’ko hannunta tayi’ko’karin zamewa ya matse hannun murya a ‘kasa yace”Deejah yau mantawa aka yi da abincinka?” Wani kallo tayi masa kafin hawayen idonta su zubo. Hawayen ya dinga bi da ido “ kukan na menene?” Murya can’kasa tace “ abincinka yana wajen amaryarka” fuska ya sake tamkewa kafin yace “ wace irin magana ce wannan? Kema kin san sarai ba da amincewata aka yi aurennan ba, to me yasa zaki damu kanki yarda ta shigo haka zata koma, bani da tsarin ajiye mata biyu a gidana, ba ra’ayina bane tashi muje ki bani abinci kada ki sake’bata min rai” Ya jata ya mi’kar tsaye suka fita. Hanyar part d’insa direct suka nufa. Dai-Dai lokacin hafsa’yar hajjan ta ganosu itace auta a d’akinsu da sauri taje ta sanar da hajjan. Hajja kuwa tayi saurin fitowa fad’i take muje ba dani za’a yi wannan iskancin ba muje da kaina in kai masa amaryar in kuma nuna masa ni Na haifeshi ba shi ya haifeni ba... A bakin ‘kofar part d’in nasa ta tsaya tana buga ‘kofar da ‘karfi kamar zata ‘balle ‘kofar. Dahda ransa a ‘bace ya bud’e ‘kofar, murya a sar’ke yace “Hajja lafiya?” Kallon sama da ‘kasa ta jefa masa “ sannu isashshe har kana da bakin tambayata lafiya to ita lafiyar tana gidan ubanka wuce muje ka taho da amaryarka ita ta cancanta ta kwana a d’akinnan sai an mata kwananta uku rus da bazawara ta bata, kuma ban amince da ko bakin’kofar nan naga sillan’kafafunta ba wuce muje ka taho da matarka.” Mommah da take cikin parlourn tana jiyo duk abinda yake wakana ta mi’ke zaune zauciyrta na tafarfasa ta fice daga palrlourn. Shatu dake zaune a main parlour tana jiyo duk abinda yake wakana tayi al’kawarin yau tsohuwar nan ba zata kwana da lafiya ba. Ta shige d’akinta tana’kissama irin abinda za tayi mata. Da sauri ta shiga tanadin kayan duk da zata yi amfani dasu. Cikin dare ta nufi d’akin da aka sauke hajja, a hankali ta murd’a’kofar Ta shiga, Hajja ta tarar ta saki baki tana barci taci sa’a kuwa hajjan ita kad’aice a d’akin tabbas shirinta zai tafi yarda take so, Ta sake kallon shigar da tayi a mudubi’kusumbi tayi sosai a bayanta ga gashinta da ta saka ya rufe mata fuska gaba d’aya sai wani farin hjibin momma da ta sin’kife jikinta dashi, ba’a ganin fuskrta Sam, Ta dur’kushe sosai kamar wada tana lan’kwashe ‘kafarta kamar a shanye take. Tsaye tayi gefen gadon hajjan kafin tasa sandar hannunta ta zunguri ‘kafar Hajjan “ Ke tashi ajalinki yau yazo tsohuwar banza mai takurawa jama’a....... A razane Hajja ta rusa wani ihu fad’i take “ ku kuke ganinmu ba mu muke ganinku ba innahu ala raja’ihi la’kadir...... [8/21, 11:27 PM] Aysha📚: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -10 Sosai Hajja ta sake razana ganin shatu tana nufota, fad’i take “ Don Allah kada ku cutar dani ku fad’i mai kuke so nayi? Ni baiwar Allah ce ba ruwa na da kowa a duniya.” Shatu ta ‘kya’kyata wata mahaukaciyar dariya “ so muke kada ki sake cutar da hadizatu idan kuma kin’ki zaki ga sakamakon taurin kai kina ji?.” Da sauri hajja ta d’aga kai “ Na bi Allah na biku insha Allah ba zan sake komai ba” shatu ta sake kecewa da dariya bayan jin abinda tace cikin daka tsawa tace “ To rufe idonki kuma kada ki sake ki bud’e sai nayi nisa da tashi sama.” Da sauri hajja ta rintse idonta gam, shatu da sauri ta fice daga d’akin ta shige d’akinta. Ai cikin azama hajja tana bud’e idonta tayi saurin mi’kewa ta fice daga d’akin jikinta har makyarkyata yake, A tsakiyar falon ta tsaya ta dinga kwalawa mutanen gidan kira. Yarda muryar tata ta karad’e gidanne yasa d’aukacin mutanen gidan fitowa, suka tarar da ita a dur’kushe hankali tashe suke dubanta. Dahda ne yayi’karfin halin cewa “lafiya hajja?” Hajja ta zuba masa wani irin kallo “ ina kuwa lafiya ko da yake yanzu ba zan yi magana ba sai da safe kai ni falonka a can zan kwana kuma kana zaune daga gefe na Yau gamo nayi da aljannu a gidannan.” Dariya ce taso kama Ammar ganin yarda ta ha’ki’kiance take’buya a bayan dahda. Momma kuwa baki ta ta’be ta juya ta koma ciki bayan tayi wa amaryar mijinta kallo d’aya. Ita kuwa amaryar bin bayan mijinta tayi tana tsinewa hajja a zuciyrta yarda zata’bata mata daren amarci duk da tanadin da ta shirya masa ga turarukan tsubbace tsubbace da ta ambula a jikinta banda wanda ta turara sai da ta kusa samo kan mai gidan sannan wannan tsohuwar zata rusa mata shirinta. ‘Karfe bakwai nayi Hajja ta fito babban falon gidan bayan ta tasa ‘keyar dahda a gaba “ Muje ka had’o min kaf kan ahalin gidannan ina da magana dasu “ cikin tausasa murya yace” Hajja da kin bari gari ya ‘kara wayewa ....” “ Na’ki Na bari garin ya waye ahmadu nace na’ki Na bari manga uba na, saboda ba kai kayi gamo da abinda Na gani ba ko.” Tayi saurin tare shi da sababin fad’a. Shiru kawai yayi yabi bayanta zuciyarsa fal ‘bacin rai don dai uwa uwa ce da ba wanda ya isa yazo gidansa ya aikata masa haka. A tsaye suka tarar da momma tana sake gyara cushions d’in main parlour d’in tas ta gyara gidan sai’kamshin turaren wuta gidan yake. Dahda ya bita da kallo ganin yarda tayi kyau sosai cikin wani pink lace duk da fuskarta ba fara’a amma dai bata fasa gaisheshi ba, sannan ta’karasa gefen hajja da take zaune saman kujera ‘kafa d’aya kan d’aya tana girgiza jiki fuska cike da masifa, muryar mommah a cunkushe itama tace “ Hajja barka da safiya an tashi lafiya?” Sai da Ta ‘kare mata kallo sama da ‘kasa cikin masifa tace “ ‘kalau sumul na tashi duk da ba haka kika so ba, cikin kiyayewar ubangiji na tashi lafiya, saboda kin san tsaye nake akan ‘kafafuna wajen ibada, wai ke deejah har tsubbun taki ta kai ki fara turawa mutum aljannu ? Saboda Na saka d’ana yayi aure, to albishirinki wannan auren mutu ka raba kuma idan kin tashi yau da daddare ki turo min sarkin rauhanai ma ba aljannu ba , Aljannun naki mai suka isa suyi min sunzo sun baki labarin yarda Na fatattakesu da ayar Allah.” Shatu da sauri ta juya Ta shige kitchen saboda dariyar da Ta ciyota. Hajja Ta cigaba “ kuma ni da gidan d’ana ba inda zani zama daram.” Mommah shiru tayi tana al’ajabin hajja yau kuma gingimemen sharrin da za tayi mata kenan lallai tsanarta da hajja ta girmama. Hajja ta juya gun Dahda “ kai kuma manga kana tsaye baka tambayeni ba’asi ba, yo ai dai kace hajja mai ya faru kike wannan fad’a da safiya haka tunda kai haka Allah yayi ka kamar d’an fari, to ko Mahmud da yake d’an farin baya abin da kake. Wato kana ji cikin dare matarka tayi min turen jinnu wai suna gargad’i na na rabu da hadizatu kaji fa wai dijah yanzu har tayi shaharar turo min Jinny?” Dahda ya girgiza kai saboda ‘bacin rai ma kasa magana yayi ya zuba mata ido kawai. Ammar ne cikin d’aure fuska yace “ ko dai mafarki kika yi hajja ina mommah taga aljannun da zata turo miki? Mu tunda muke gidannan ba wasu aljannu.” Girgiza kai hajja tayi sai kuma tace “ Ba shakka, ‘karya nayi maka kenan? To manga ubanka da yake zaune shine ma’karyaci ba ni ba. Ra’ayal aini yarda nake ganinka haka naga aljannu ina tofa musu addu’a suna ihu da tumami suna fad’in deejah ce ta aiko su, haka Na ‘konesu ‘kurmus ba mamaki idan kuka je d’akin ma kuka ga haya’kin da tokarsu, yo ni za’a kawowa zancen banza aljannun me Allah na tuba”. Ba wanda ya sake mata magana haka ta mi’ke ta koma d’akinta tana sake bambamin tijara. Shatu da take la’be a bayan ‘kofar kitchen ta girgiza kai had’e da yin ‘kwafa ta juya ta shige d’akinta . ‘Karfe biyu daidai ba’kin Abuja suka sauka. ‘Kannen mommah ne hisham da hafsa sai nahnah. Kyawawa dasu farare tas kamar su innaji da mommah. Shatu tana zaune tana lesson driver ya dawo daga’daukosu d’aya bayan d’aya suke bin ta da kallo ita ma tana kallonsu, Hisham ne ya bud’e mata alamar ta taho ya dube ta kafin yace If I guessed It right you’re shatu ?na canka shatu ce ko?” Da sauri ta d’aga kai hisham da su nahna suka rungumeta da ihu cikin tsananin farin ciki suna murnar ganinta hakanne Yasa Ammar da mommah da imran saurin fitowa suna murnar ganinsu , kasancewar sun dad’e basu zo hutu ba nahna da hafsa suna turkey, shi kuwa hisham mate d’in Ammar ne tare suka gama makaranta a egypt, Imran ne yayi oxford university england. Murna da hayaniyar da suke ce a main parlour ta fito da mutanen gidan har Hajja da ta fito tana dogara sandarta da yake tana da ‘kiba ciwon’kafa ya sata a gaba. ‘Daya bayan’daya take hurga musu kallo tana amsa gaisuwarsu a gatsine “ Ba shakka dijah kin ci gida kin mallake manga kin mallake dukiyarsa ga ‘yan uwanki ma sun zo sun taru a gida, kai Allah wadaran naka ya lalace su kuma wad’annan gand’an-gand’an ‘yan matan daga ina?” Nahna fuska a d’aure za tayi magana mommah ta girgiza mata kai “ Don’t say any word here ku shiga part d’ina am coming.” Kasancewar akwai tarbiyya hakan yasa basu shiga ba suka ja hannun shatu su kayi gaba su imran ma suka bi bayansu. Mommah ba tace da hajja komai ba ta mi’ke zata wuce. Cikin masifa Hajja tace “ la shakka ga ‘yar iska wato kin bawa banza ajiyata nayi tayi ko? To kinyi da gyatumarki mai kama da sadakar yallar nan kuma da ni kike zancen yau yau zasu juya su koma, kuma kaf jakunkunansu sai nazo Na caje don yanzu haka wani tsubbun suka kawo miki an ji anyi miki kishiya azo a koreta ko? Kuma idan zasu tafi ki tattara har bararojinnan su tafi da ita shaid’anun banza kawai.” Momma wani abu Ta had’iya kawai ta juya ta shige part d’inta zuciyarta na tafarfasa, itama fa mutum ce ba dutse ba dole zuciyarta zata dinga zafi da irin cin kashin da hajja take mata amma ya zata yi dole ta girmamata tunda d’anta take aure. Sai da Ta share hawayen fuskarta sannan ta’ka’kalo fara’ar dole ta bud’e’kofar falonta. A zazzaune ta samesu tuni sun watsar da lamarin hajja sun saka shatu a tsakiya, sai fito mata da tsarabar kayayyaki suke wanda suka siyo mata a turkey da wanda kakanninta suka bata, sai nuna mata tsananin soyayya suke, hakan yasa fara’ar fuskar shatu ta kasa ‘boyuwa kowa nuna mata ‘kauna yake ashe ba zata yi maraiciba bayan mutuwar innaji, ashe yanzu ne zata fara fuskantar farin ciki a rayuwa. Ta lura kowa sonta yake idan ka d'auke Imran da yake gefe yana harararta ‘kasa-‘kasa. Hisham ya dubi Mommah kafin yace “ Hope dai by now an yi mata register a school ?“ Momma ta girgiza kai “ so muke brain d’inta ya da’n bud’e before taking her to school insha Allah” Imran ya ta’be baki cikin takaici yace “ Allah wahala kawai kuke wannan yarinyar she will never be socialized kamar yarda kuke so , rayuwar daji fa tayi ai sai a slow kawai dama kun daina wahalar da kud’inku kawai don wasting time dinku zaku yi ji fa wasu tarkace a hannunta “ ya fad’a yana nuna hannunnata, gaba d’aya gurin shiru kawai su kayi zuciyarsu kowa da mamakin imran. Hisham ne ya katse shirun yana dafa Imran yace “ Amma son banyi expecting hakan daga wajenka ko bakomai she is your bloody sister da nake fatan mu nuna mata soyayya mu kuma bata jin dad’in da ta rasa.” Tsaki yayi Hasfa ganin yarda mommah ta damu sai ta sako wasa cikin zancen “ Rabu dashi Yaya hisham bayan ma bai san yarda rana zata fad’i ba “ da sauri ya zaro ido “ wa? God forbid wallahi insha Allah rana a gabas zata fad’i ko don ba kiga babban kamun da nayi ba classy baby ga good hygiene ga kyau ga ladabi.” Tsakin da mommah ta zabga ne yasa yin shiru duk gurin kuma aka saka dariya ban da shatu da imran ya riga ya ‘bata mata rai. Mi’kewa tayi zata shige ciki taji Nahna tana cewa “ Mhmn Allah ya kaimu lokacin da zaka zo kana’yar murya “ ya mi’ke yana fad’in “ ai ko a ‘kafa aka d’aura min wallahi sai na cire na yar “ Mommah kwafa tayi tana nuna musu dinning “ Hisham close the chapter kuyi taking shower ku ci abinci duk da dai tafiyar dad’i kuka yi tafiya a jirgi” Nahna tace “ Yo wa zai zo kano from Abuja a mota.” *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -11 ELEGANT ONLINE WRITERS..... Da yammacin ranar kuwa ‘yan matan mommahn gaba d’aya suke a kitchen suna tayata d’ora sanwar dare, shatu na gefen Nahna tana tayata had’a salad. Ta dubi antynnata kafin tace “ Anty Nahna ku nawa ne’yan uwan innaji?” Nahna murmushi tayi tana dafa gashin kan shatu data gyara mata shi ya sauka har tsakiyar gadon bayanta. “ Mu biyar ne Mommah ce babba sai adda maryamu sai hamma hisham sai ni sai kuma hafsa shekara d’aya ne tsakaninmu da hafsa. Mu kad’ai ne a gidanmu babanmu bai kara aure ba shi yasa sam ba abinda yake d’aga mana hankali bamu da yawan da za’a samu sa’bani a cikinmu muna son junanmu kamar mu had’iye kanmu, shi yasa sam ba muyi Farin ciki da auren da ammar zaiyi ba, mun so ya auri jininmu ta yarda zamu sake tashi tsintsiya mad’aurinki d’aya, amma hakan bai yiwuba kana tasa Allah na tasa amma Allah’s plan is better than ours right?”murmushi shatu tayi ‘kaunar dangin innajinta yana sake ratsa ta musamman ganin yarda suke nan nan da ita. Sai kuma ta kama hannun nahna race “me kika fad’a daga ‘Karshennan ina so in iya irin maganar nan” Nahna ta sake sakin murmushi kasancewarta ma’abociyar murmushi, tana jan hancin shatu tace “ kin san turanci?” Shatu Ta d’aga kai “ Na sani innarmu idan tana koya min karatu tana yawan ce min sai na iya abcd sannan zan iya turanci “ Nahna tace “ To wannan maganar da nayi shine turanci kice kin iya abcd?” Shatu cikin dariya tace “ kai na iya fa har’karshe kuma har rubutu na iya da karatun hausa Na abcd kuma na iya su boy girl, man da woman kai har su cup fa na iya.” Da sauri hafsa da mommah suka juyo nahna kuwa murmushi tayi kice “ yarinyar tawa kanta na ja ba zama kiyi wuyar shiga school ba.” Momma farin ciki ya cikata “ai kuwa gobe za’a miki register a school ko primary 4 su kaiki shekara nawa kika ji innajinki na fad’ar shekarunki?” Shiru tayi tana lissafi sai tace “ haka dai da zata mutu ina shekara sha uku “. Hafsa tace nawa kenan a karatun book?” Wani kallo tayi mata tace “ kai mhmn thirteen d’inne ban sani ba aradu har dubu munje da innaji tace min thousand sunansa “ gaba d’aya suka hau tafa mata. Momma cikin farin ciki ta jata ta rungumeta tace “lalle maryama tayi ‘ko’kari am so proud of her .” Shigowar amaryar dahda ce ya dakatar dasu daga hirar da suke, ko magana bata yi musu ba ta bud’e fridge tana wani gatsine sai kuma Ta d’aga waya murya cikin kissa take fad’in “ Am coming dear naje samo maka drink d’in da kace ne.” Tana fad’a tana kallon mommah da take murmushi ‘kasa-‘kasa, “0key dear yanzu zan dawo kada ka damu zan maka abinda yafi kis.......” wani kallo mommah tayi mata da yasa ta gintse abinda tayi niyyar fad’a ta juya har ta kai ‘kofa momma tace “ kice masa har ya dawo daga kadunan da ya tafine? Kuma yaushe ya fara shan drinks na general kitchen..” wata kunya ce ta kama amarya ta juya da sauri ta fice, gaba d’aya suka saka dariya a kitchen d’in mommah tace “ kaji min shashasha right now fa na gama receiving call d’in and he told me yana kaduna amma kaji makira “. Suka sake she’kewa da dariya. Nahnah tayi tsaki “ Ni ba’kin cikina d’aya mommah da kuka amincewa imran ya auri ‘yarta ba kiyi masa jan ido ba, don sun ga d’anki ya taso da nasibi ga arziki ta ko ina ‘karuwar masa yake, kuma sun lura da matsanancin son da yake miki shi yasa fa suka shiga jikinsa idan ban da haka ina imran ina wannan yarinyar tana tafiya kamar bulala, ji fa ranar da muka had’u da ita a mall wallahi nunawa tayi bata son mu ba.” cikin takaici momma ta girgiza kai “ ki rabu da imran taurin kai gareshi kamar mutanen farko sau nawa na nuna masa bana so sau nawa na hanashi, amma ya’ki jin zancena amma lokacine zan nuna masa bashi da wayo daga shi har dangin ubannasa, muje dai zuwa a kuma juri zuwa rafi....” Ita kuwa amarya tana fita d’akin hajja ta shiga ta zauna ta gaya mata’karya da gaskiya hajja ta hau kai ta zauna. “ kika ce sun zageki zainabu?” Amarya Ta d’aga kai hajja ta kuwa mi’ke zaune “ Ai kuwa tunda suka zageki ba ke suka zaga ba ni suka so zaga aka fake dake, to kuwa ba zai yiwu ba uwarki ni na sha mama na bar mata ban ga d’an abu ta kazar uban da zai zagar mana mahaifiya na ‘kyaleshi ba ke ko da kuwa sadakar yallar uwarsu ce muje madafar “ Amarya farin ciki fal ranta ta mi’ke ta bi hajja kitchen. Tsaye hajja tayi ri’ke da ‘kugu tana musu kallon sama da ‘kasa “ Eeh lallai kuwa ba shakka na ta’kar’kare na d’au cikin manga, Na sha ba’kar wuya a haihuwarsa ashe dai ku na haifawa, an shigo cikin daula a dafa wannan a sauke wannan,A samu na banza aci ai nak, bama wannan ba uban me zainabu tayi muku kuka zageta? Ko kuwa sa’kon zagin kuka bata taje ta isar min hamsha’kai ?” Shatu ta zaro ido tana kallon amarya murya ‘kasa-‘kasa tace “ Allah ya shirya babba da ‘karya cab” gaba d’aya kitchen d’in ba wanda bai ji maganarta ba har hajja. Amarya ta zaro ido “ ke don ubanki ni nake miki ‘karya ko hajja?” Shatu Ta sake gyara zama tace “ duk wanda yayi ‘karyar ai addu’a nayi “ a sukwane ba suyi auneba suka ga ta zuba wa shatu mari hannu bibbiyu a zafafe hafsa ta janye ta tana mata wani banzan kallo “ kada ki sake ki sake dukanta me tayi miki? “ momma ta nuna musu hanyar ‘kofa “ ku fita “ ta’kofar baya suka fice sannan ta kalli hajja “ kiyi ha’kuri ba wanda ya zageta amma tunda ta fad’a miki kin yarda Allah ya baki ha’kuri” daga haka Ta fice bayan ta watsa wa amarya kallon banza. Hajja bata shiga d’aki ba anan main parlour ta dinga zazzaga tijara zagi ta uwa ta uba ta dinga aikawa su mommah bayan amarya ta zauna ta sake fonfata wai har taji sanda suke cewa so suke ta mutu su sake mallake manga gaba d’aya har dukiyrsa hakan yasa ta sake sauke kwandon tijara zagi ta uwa ta uba. Ran shatu ya’baci musamman ganin yarda su nahna suka fara had’a kaya wai tafiya zasuyi da sassafe zasu bi flight d’in safe su tafi, haka ma hajiya mama tace bata son tashin hankali su taho kawai. Shatu kuwa ta’kudirce a ranta tsohuwa hajja ba zata kwana lafiya ba sai Ta gwammace kid’a da karatu. Cikin dare shatu ta mi’ke daga gefen nahna da suka kwana tare a d’akinta, sad’af-sad’af ta fice. Murd’a ‘kofar hajja tayi a hankali ta shige ta mayar da ‘kofar ta rufe, dubanta ta kai kan hajja da ta saki baki tana barci tayi, har da yawun barci ta saki dariyar mugunta bayan ta kashe fitilar d’akin da fanka har da a.c . ‘Dif d’akin ya ba’kunci duhu ga windows dama duk a rufe, shatu ta shige ‘kar’kashin gadon hajja a hankali, kasancewar ba auki ne da ita ba zuruf ta shige . Muryarta ta kumbura ta fara fad’in “ke tsohuwa ke tsohuwar banza tashi maza ajalinki yazo....” Hajja da taji maganar daga sama a razane ta farka taji d’akin d’uf misalin dai duhun kabari da ake fad’a . “Kada ki sake kiyi mana ihu ba dai kince kin ‘konamu ba zuwa mu kayi ki ‘kara ‘konamu mun ja kunnenki ba kiji ba to yau a tsakiyar dajin aljannu zaki kwana kafin gari ya waye mu zu’ke jininki.......” Hajja jikinta ‘bari kawai yake murya a razane take fad’in “ Hajja kwananki ya’kare idan ban da shegiyar ‘karyata dama mai ya kaini cewa nayi fad’a da aljannu......😂😂🤣🤣🤣 Kai yau nayi typing da yawa so that ina jiran in ga ruwan comments. *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -12 ELEGANT ONLINE WRITERS.......... Shatu tayi saurin matse dariyar da take son kamata, ta sake jijjiga ‘kasan gadon , cikin murya mai amo sosai tace “ Baki ga komai ba tsohuwa sai kin bud’e ido kin ganki a gaban sarkin aljannu yana bada umarnin a shanye jininki a yar da gawarki a daji namun daji su cinye ba dai ba kya jin magana ba mun ce ki fita daga harkar hadizatu kin ‘ki hahhhhhahhhha yau zamu sha jini ku ‘karaso maza ku d’auketa kada ku sauketa sai a dajin sarki ‘kuraizu hahhhhhahhha.” Ta sake tuntsirewa da shegiyar dariya hajja kuwa tuni ta sume tun bayan da Ta ‘kwallara wata ‘kara da duk gidan ya amsa bayan taji an jijjiga gadon da ‘karfi. Imran ne ya fara fitowa kafin su mommah suma su fito kowa yana Duban d’akin hajja inda ‘karar take fitowa. Imran baiyi wata wata ba ya bud’e d’akin da sauri ya ‘karasa gun hajja da ya gani a san’kame akan gado, ya fara jijjigata sai dai ba alamar numfashi a tare da ita, idanunsa ne ya sauka akan tsinkakken abin hannun shatu da sauri ya zaro ido bayan ya d’au abin hannun yana dudduba inda zai ganota, bai ga alama ba ya zira abin hannun a aljihunsa. Momma kuwa da sauri ta ‘karaso tana dubata a gigice take sosai hakan yasa murya na rawa take cewa “ Imran kira doctor she is unconscious “ Imran ya mi’ke yayi saurin shiga toilet nan ma bai ga shatu ba, ruwa ya d’ebo ya zubawa hajja a jikinta ,da sauri ta kawo ajiyar zuciya ihu take tana fad’in kada ku tafi dani bijahil kudrati na daina shiga sabgar dijama innalillahi.” Kowa d’akin tsit yayi yana kallonta, Imran ya kamata “ Tashi Hajja ba wani aljannu da izinin ubangiji koma akwai zan binciko su” Hajja ta mi’ke jikinta sai ‘bari yake fad’i take “muje d’akinka imran tunda manga baya nan a can zan kwana ni da d’akinnan har abada anan matattarar aljannun gidannan suke.” Ammar da yake gefe ya tuntsire da dariya sannan yace “ Hajja rannan fa cewa kika yi kunyi fad’a dasu har kin ‘konasu to yau me yasa kika kasa.” Shiru tayi tana dube-dube “ kai Ammar ka iya bakinka yanzu d’akin nan taf yake da jinnu kafin kaima su dawo kanka muje lmrana” jikinta rawa yake sosai Imran ya fita da ita daga d’akin. ‘Dakin mommah ya nufa da ita da sauri taja tunga ta tsaya “ ina zaka kaini Imran?” Fuska a had’e yace d’akin mommah mana wani abu ne?” Hajja taja baya kafin tace “ma’ana so kake naje d’akin su samu nayi su dagargazani d’akinka zaka kaini dama manga na nan ne sai ba kwana a d’akinsa gobe kuwa jirgin asuba zan bi zuwa garinmu ba zan sake kwana a gidan manga baseries kuyi min bukin na tikitin jirgi.” Ammar yace “kice ba zaki zo bikin bros ba?” Kallonsa tayi sai kuma tayi ‘kwafa ta dam’ki hannun Imran “muje d’akinnaka” Imran ya’bata fuska Kafin yace “ Ni fa hajja ba’a shigar min d’aki ni kad’ai nake amfani dashi for goodness sake ya zanyi dake idan kin so shiga toilet ki dai canja shawara idan ba zaki shiga d’akin mommah ba sai dai a kaiki d’akin amarya” “To kaini can d’in ita ‘yar banza ma ko fitowa ba tayi ba duk wannan budirin da ake.” Shi dai baiyi magana ba ya jata ya kaita part d’in amarya . Yace “sai ki buga mata ni zan tafi na kwanta” ya juya da sauri ta cakumoshi ganin labulai na motsi, tsaki yayi sai kuma ya hau dukan’kofar amarya tana fitowa ya bar hajja yayi saurin fita so yake yaje ya rutsa yarinyar can. Ko da ya shiga d’akin ganinta yayi kwance akan gadon hajja tana ta tuntsira dariya, ko kad’an bata damu ba da taga ‘kofar d’akin a rufe da key bata da hanyar fita ta san kuma dole goben asirinta zai tonu. Tsit tayi bayan ganinsa a tsaye kamar wanda aka turo fuskarsa a had’e kamar hadarin kaji. Gadon ya’karasa ya janyo jelar gashinta sai gashi ta mi’ke tsaye tsam, fuskarta babu alamar tsoro ko kad’an. Ji yayi kamar ya mammaketa ya ja bakinta ya murd’e duk da taji zafi bata nuna masa ba sai ma ‘bata fuska da tayi “kece aljannar da ke tsorata Hajja kenan to yau asirinki ya tonu kuma sai na gayawa kowa abinda kika aikata har dahda so kike ki kashe masa uwa kenan?” Turo baki tayi tana masa kallon ‘kasa-‘kasa, ba tare da tayi magana ba, ya sake janta ta durgo daga kan gadon sai gata a gabansa, kallon mamaki yake mata ganin yarda sam ba tsoro ko kad’an a tare da ita ya rasa irin yarinyar nan ko dai da gaske tana da ala’ka da jinnu tunda ance rayuwar daji tayi. “Wato ke baki tsorata ma da laifin da kikayi ba, ji yarda kike kallona da idanu kamar na mayu d’auke idonki a kaina before i nock your head, yau a toilet za kiyi spending darenki wuce Muje.” Ta’be baki tayi an gaya masa tana tsoron kwana a toilet ne balle wannan toilet d’in nasu na ‘yan gayu ita tsoronta d’aya kada ya gayawa wannan Almasifatun Babannasu da ko idonsa bata son gani razana ta suke. Ya turata toilet d’in har zai kashe fitila da yake switch d’in a waje yake sai ya fasa ya rufe toilet d’in da key ya fice daga bed room yana mamakin taurin zuciyar shatu. Da asubar fari yazo ya bud’eta ba don komaiba sai don baya son ya shafawa mommah black paint dole zai bar hajjan a zuwan jinnun gaske ne. Tana barci a kwamin wanka ya sameta hankalinta kwance. Tsayawa yayi yana kallon al’ajabi yarda take barci peacefully a cikin toilet idan shine ai an kasheshi baya jin zai kwana da lafiya. Ya daddage ya d’aka mata duka, ta d’anyi saurin bud’e idonta tana ganin shine ta saki murmushin mugunta don tayi targeting sai ta rama wallahi nan kwana kusa kuwa. Ta zuro’kafafunta ta fita. Shi kuma yabi bayanta. Sai da yaga ta shiga d’akinsu sannan yaja ‘kofar part d’in hajja ya fice masallachi. Ana idar da sallahr asuba Hajja ta fito main parlour ta zauna, ko tunanin d’aukan kayan ta bata yi ba. Imran yana shigowa daga masallachi yayi arba da ita dariya taso ‘kwace masa sai dai da yake ba ma’abocin dariyar bane sai ya gimtse “ wai meye haka hajja tafiya ba shiri” ya fad’a yana jingina da bango. “ mi’kewa hajja tayi tana gyara sandarta kafin ta sake gyara glass d’in idonta ta kafeshi da ido kafin tace “ko ubanka manga bai isa yace sai na sake kwana a gidannanba aljannu na neman kassarani maza-maza muje ka kaini tashar jirgi.”Ransa a ‘bace ya juya sai kuma yace”ai dai kya yi sallama da mutanen gidan.” Ya shige sashen mommah Hajja tayi saurin bin bayansa “muje ka wani bar ni anan nifa tsoron gidannan nake ji” shatu da take la’be a window ta tuntsire da dariya da sauri hajja ta dam’ki hannun sa “kaji ko wallahi har yau suna gidannan ko baka ji abinda naji ba” hararar shatu yayi tayi saurin sakin labilan. Nahna da take zaune tana azkar ta kalli shatu “ ke lafiyarki kuwa?” Shatu taso bata da labari sai kuma ta gintse tace “zo kiga tsohuwar nan anty nahna zo kiga yarda take rawar d’ari duk tabi ta ma’kal’kale yah Imran” Nanah tace “Allah ya shiryeki shatu ko dai ke kike tsorata ta?” Da sauri shatu ta girgiza kai. Suna kallo su mommah suka rakata su kayi mata sallama. Kashegari kuwa budurwar Imran ce ta bayyana a gidan tazo hutu a cewarsu wajen uwarta daga abuja fara ‘kal da ita har yellow take sai dai a tsaye take tsam kamar sanda shatu da take jikin window inda ta saba la’be, tana ta kallon yarda Imran yake rawar ‘kafa da budurwarsa ta kuwa ta’kar’kare tace “Muciya da zani” kasancewar parlourn ba hayaniya ba wanda bai ji furucinta ba sai da maganar ta fito tayi saurin toshe bakinta tana kallon Imran da suka yi four eyes da ita ransa a matu’kar ‘bace.....” To fah! Shatu danger *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -13 Da sauri shatu ta ruga part d’in mommah, shima Imran yayi saurin mara mata baya, yau kam ba mai hanashi cin kwal uban shatu, a bayan mommah ya ganta tana ta dariya ‘kasa-Kasa, kamar mayunwacin zaki haka ya bita zai cafkota, mommah tayi saurin ri’keta tana furta “kai lafiya uban mai tayi maka?” Cikin ‘bacin rai yace mommah please ki rabu dani in jibgi yarinyar nan, habibteey fa take tsokana wai muciya da zani” dariya ce taso kufcewa mommah tayi saurin rufe baki wanda hakan ya sake ‘kular da Imran yayi kukan kura ya kamota mari lafiyayye ya sauke mata. Da sauri mommah ta janye ta ranta a matu’kar ‘bace “ wai meye haka ne Imran kasheta zaka yi akan wata habibty to wai ma da tace mata muciya da zani sunanta ne? Ko kuwa an canja mata suna ne ta koma muciya ina ce dai ba sunan mutum bane muciya?” Ransa a ‘bace yake sake kallon mommah kafin yayi ‘kwafa wallahi da ita take kuma zaki gane baki da wayo” Mommah ta’kunshe dariyarta ita da nahna da shigowarta kenan tace “a’a Imran kaso kanka sai dai kuma idan tsarguwa kayi ni ban ga abin damuwa ba indai ba habibteeyn taka tayi kama da muciyar da zani bace” Hafsa da Nahna suka tuntsire da dariya. Tsaki Imran yayi ya juya ya fice zuciyarsa cike da sake tsanar shatu. Bai ganta ba a parlourn hakan ya nuna masa ta shiga sashen mahaifiyarta don haka direct d’akinsa ya nufa yana danna waya nemanta yake, sai dai sai rejecting calls dinsa take. Ita kuwa tana can zaune fuska a tur’bune tana kallon mahaifiyarta “amma anty wannan yarinyar wacece? A gaban mutane fa ta disgani wai muciya da zani yanzu idan tasa Imran ya ankare da halittata fa ya fasa aurena” zainabu ta girgiza kai “bai isa ba bashi da wannan right d’in baby don na riga Na d’inke zuciyarsa a jikin taki tsaf ba zai ta’ba kallon wata mace bayan ke ba da sunan so” murmushi ta saki “wallahi na yarda da lamarinki anty gashi nan ma yanzu sai kirana yake tun d’azun na tabbata ya kasa sukuni ne”zainabu ta girgiza kai “ba zaki gane irin yarda na tsani Dijah bane saboda ita fa manga ya’ki aurena har an saka rana ta da yana had’uwa da ita yace ya fasa aurena bayan na tabbata ba yin kansa bane tsubbun su na fulani ne ya kamashi” Shaheeda ta girgiza kai “kullum fa anty sai kin bani labarinnan ko hadda ne yaci ace by now nayi haddarsa ni yanzu damuwata ayi a saka ranar nan na kama shi a hannuna ina son Imran to the extent.” Zainab ta dafa ta “shaheedah na sani na san kina son Imran amma fa bana so ki sashi sosai a zuciyarki don bana son lokacin da aikina zai kammala ki kawo min cikas bance kada ki so shiba a’a nafi so ma ki so shi sosai ko bakomai ba ko don dukiyarsa yaci a soshi, duk da kema na san don hakan kike sonsa da bashi da ko sisi ko shine aljannu don kyau ba zaki aureshi ba,aurenki da Imran ba fashi don nima shine burina, sai dai ina da wata manufa mai ‘karfi akan haka kuma kada ki sake ki bijire min a lokacin da bu’kata ta tazo” shaheeda murmushi tayi kafin ta janye jikinta ta mi’ke tsaye ta furta “Allah ya nuna mana lokacin bari inje in gaishe da inlaw ta kada tace bani da kunya.” Zainabu ta had’e a rai a zuciyarta tana tunanin lokacin da zata cimma burinta da ya jima a zuciyarta. Murya can ‘kasa tayi sallama a ‘kofar parlourn idanunta akan shatu tana jin tsanarta a ranta. Momma ta amsa mata sallamar fuskarta ba yabo ba fallasa su kuwa su nahna ba wanda ma ya kalleta. Sum-sun har ‘kasa ta dur’kusa ta gaida mommah. Amsa mata mommah tayi fuskarta fal fara’a tace “Ya gida ya mutanene gidannaku?” Kanta a ‘kasa tace “lafiya lau” hafsa ta bita da wani kallo a zuciyarta tace munafuka. Shatu kuwa ‘kara ‘kare mata kallo take tana son ganin wani aibu a fuskarta sai dai bata gani d’in ba fuskarta ba yabo ba fallasa tana da kyau dai-dai nata sai dai daga ganin goshinta kasan bata da gashi tsam ta mi’ke “mommah bari na kawo mata ruwa” momma ta gyad’a kai “kin kyauta kuwa mah girl hakan yayi” Shigowar Imran yayi daidai da kawo mata ruwan da tayi. Yana ganinta yayi saurin had’e rai. Ita kuwa shatu bata ma san yana yi ba ta isa gabanta ta ajiye mata ruwan ta kuma ‘ki yarda ta kalleta ta hau zuba ruwan, da azama Imran ya ri’ke hannunta. “Kwashe ruwan nan ki tashi daga nan kafin nayi ball dake wa yace miki ita ‘kazamace da zata sha ruwanki.” Kallonsa shatu tayi kallon da bata ta’ba yi masa sai taji zuciyarta ta buga bata ta’ba ganin zahirin kyansa ba sai yau da suka yi so close dashi, taushin hannunsa a cikin nata yasa ta zubawa hannayensu ido. Kamar a mintsineshi da sauri ya janye hannunsa, itama shatu hakan ya fargar da ita ta janye idonta da sauri ta mi’ke jikinta a sanyaye tayi hanyar d’akinta. Mommah kuwa ranta ne ya’baci tunaninta haushi shatu taji daji saboda furucin da Imran yayi a Kanta.mi’kewa tayi ita ma ta bi bayan shatunta. A kwance ta ganta akan gadon. Ta zauna a bakin gadon taja ‘kafarta “ Tashi shatun mommah tashi maza kije ku tafi da nahna za tayi miki shopping d’in school.” Da sauri ta mi’ke tana murmushi “mommah yaushe zan fara zuwa?” Mommah tana murmushi tana duban shatu ta lura shatu sam bata da ri’ko shi yasa kullum take cikin walwala ko tunani da wuya ka kama ta tanayi always zuciyarta fresh take as babies hearts. Tana kallonta ta fice da d’an saurinta. Ko da suka fita parlourn tuni suka tarar Imran ya fice da gimbiyar tasa. Da sassafe shatu tayi shirin school ta fito kenan ta tarar da masu aiki a kitchen hannunsu duk hand gloves da alama uban ‘kyankyamin su ke yiwa girki. Da fara’a ta shiga tana kallon Daniel tace “ shugaban yan girki abincin waye wannan?”cikin gwarancin hausarsa yace “Babyn mommah kayi kyau wow!” Harara ta zuba masa “tambayar da nayi maka kenan?” Daniel yana dariya ta shagala da kallonta yace abincin oga Imran ne” murmushi ta saki tana dubansa ta juya ta shiga store cikin abinda bai fi second biyar ta fito a guje “daniel zo ka fita da ‘bera” daniel ya zaro ido “‘bera kace mai kyau you mean rat?” Tsaki taja “kayi sauri ka tsaya kana surutu sai ya shige wani wajen” yana shiga ta rufo ‘kofar da key “idan ka cireshi ka gaya min sai na bud’e.” Ta bud’e peppe soup ta tara yawu a bakinta ta tottofa ta mayar ta rufe tana dariya, sannan ta ciro wata leda a jakarta ta tsiyaya ruwan cikin shayin dariya take sosai “yau zamu ga ‘karsheb tsafta zaka sha yawuna ka sha kuma ruwan hammata ta.” Da sauri ta bud’e daniel jin Imran na’kwala masa kira.” Kaga ‘Beran?” Ta wurga masa tambayar bayan ta lura yana kallonta “ban ganta ba” ficewa tayi tana cewa “ta gudu kenan bagware wai ban gan taba sai kace ‘beran macece?” Not edited..... *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -14 Tun da ta ganshi a parlourn hakan yasa ta zama don taga ko zaici abincin,shi kuwa yana dinning a zaune ya had’a tea ba tare da ya dubeta ba da alama sauri yake don haka da azama ya d’aga cup d’in tea d’in ya kur’ba ya kuma bud’e bowl d’in peppe soup d’in ta zuba a plate ya kai baki yana kur’ba dad’in peppe soup d’in ya ratsa har kwanyarsa ya lumshe ido yana sake zu’ka. Dariyar da shatu ta saka ce yasa shi saurin bud’e idonsa sai kuma ya had’e ransa yana dubanta tana ta she’ka dariya har da tuntsirawa,jikinsa ne ya bashi tabbas akwai dalilin dariyar tata don haka da sauri ya ture plate yace”ke zo nan” tana ‘kunshe baki ta fara shirin guduwa “wallahi kika d’aga ‘kafa daga wajennan ko da one step ne zaki ga abinda zan miki zo nan nace.” Hantar cikinta ne ya d’uri ruwa har ta juya zata wuce ba tare da taje d’in ba taji ya dam’keta ta baya gashinta yaja taji zafi sosai don haka ta runtse ido.”Don Allah ka sakar min gashi akwai zafi fa to wai mai ma nayi maka?” Tayi maganar cikin muryar shagwaba bai mata magana ba ya jata zuwa part d’insu a parlour ya wurgata saman kujera”gaya min uban me kike wa dariya ko na baki wahala nan dai ba mai cetonki balle kice wallahi idan baki gaya min ba ko school d’in da kike zumud’in zuwa ba inda zaki”Jin yace ba zata school ba ne hankalinta ya tashi duk d’okinta da takeyi zai ruguza mata shiri ta fara rawar baki”kada ki sake kiyi min ‘karya ina da abinda zan saka a jikinki in gano gaskiya don fad’a min gaskiya kafin na gano da gaskiya.” Ya fad’a cikin’kara tsare gira. Hakan ne ya sake razana ta tayi saurin cewa “idan na gaya maka gaskiyar zaka barni in wuce school?” “Fad’i ina jinki” ya fad’a yana tsareta da ido. Ajiyar zuciya ta saki sannan tace “Don Allah kayi ha’kuri a cikin peppe soup ne na zuba yawu na a tea kuma na zuba maka ruwan hamma.....” da sauri taga yayi toilet yana kakarin amai hakan yasa ta suri school bag d’inta tayi waje a guje. Ya dad’e yana amai kamar ya amayar da kayan cikinsa ‘karshe ya fito har wani jiri yake ji kamar ya kifa haka ya kwanta akan gado yana maida numfashi har ga Allah yarinyar nan ta cuceshi cuta bata wasa ji yake kamar ya fito da kayan cikinsa ya sauyasu ha’koransa kuwa da harshensa ya dirje su yafi sau nawa har rad’ad’i suke masa zazzafi mai zafi ya kamashi haka ya ‘kudunduna a gado duk da yana da important issue haka ya ha’kura da fitar. A school an kar’beta ko da suka gwadata suka ga gwara kawai su kaita primary five tunda tana da sharp brain idan yaso a gida a samar mata lesson teacher. Da ta dawo kuwa samu tayi duk gidan suna part d’insu Imran wai bashi da lafiya ta’be baki tayi ta samu abinci kawai ta fara ci ita ina ruwanta da ciwonsa mutum sai shegiyar tsaftar tsiya har da wani amai da ciwo. Taci ta ‘koshi sannan tayi wanka ta zira da wando tana fitowa ta tarar da mommah ta shigo. Mommah ta bud’e mata hannu tana welcoming d’inta tare da furta”oyoyo autar mommah ya school d’in” ta d’aga kai “ Ba laifi mommah amma fa sai an jawa ‘yan class d’in kunne bana son rashin kunya don naji suna ce min wai ra’kumi a cikin ‘yan tsaki to yau dai nayi musu na ba’kunta gobe kuwa wallahi na jaki zasu ci” Mommah murmushi tayi ta dafa ta “ba’a fad’a a makaranta baby na kada ki kula kowa kin ji’yar albarka kiyi karatunki kawai ki koma gida shine abinda ya kaiki kinji?” Murmushi tayi ta d’aga kai shigowar nahna ce yasa mommah ta tuna ruwan tea zata dafawa Imran kuma ya ro’keta don Allah da kansa zata kawo masa don yanzu tsoron ta’ba komai na gidan yake da zai iya ma da kansa zai shiga kitchen d’in ya dafa to jiri yake ji saboda tun safe ba abinda ya shiga cikinsa.Momma ta girgiza kai “kinga kuwa nahna shaf na manta abinda nazo yi bari in tashi” Nahna tana dariya tace “ya kuwa ce da kanki yakeso ki dafa masa kuma kina juyewa in kawo masa ni ban san me ya sameshi ba” mommah tace “mhmn rabu da Imran haka yake idan yana cuta sangarta ce dashi zan ga yarda matarsa zata yi da ‘kyan’kyaminsa wallahi abin yana damuna sai kace wani mai cutar tsafta.” Da kanta ta dafa tea d’in ta bawa Nahna ta kai masa. Yana ganinta ya mi’ke zaune da kyar yana ri’ke kansa ya jingina da bangon gadon a hankali ya motsa bakinsa muryarsa ta fito “please mommah ce ta dafa kuma kina tsaye a wajen? Ibilishiyar yarinyar nan kuma bata wajen ko?” Nahna ta girgiza kai tana dariya ta tabbatar masa mommah ce ta dafa da kanta. Ta zuba ta mi’ka masa yana sipping a hankali. Lokacin shaheeda ta murd’a ‘kofa ta shigo kallo d’aya tayiwa nahna ta d’auke kai hannunta d’auke da cooler ta nufi gefen gadon ta zauna cike da kwainane sai zabga ‘kamshi take ta zauna a gefensa tana jan yatsun ‘kafarsa “am sorry Habibi ya jikin?” Nahna ta kai idonta kan hannun sai kuma ta ta’be bakinta da sauri ta fice tana mamakin rashin kunya irinta ‘yan matan yanzu sam basa iya tsare mutuncin kansu shi yasa ko auren aka yi mazan basa ganin mutunci su.shaheeda ta sake kallonsa tana murmushi “ Habibi in zuba maka abincin?” Da sauri ya girgiza kai, ta kuwa had’e rai a hankali tace “kai habibi I cooked it with my own hand fa please kaci kaji?” Cikin muryar shagwa’ba take gaya masa hakan ya sake narkar da zuciyarsa yana jifanta da wani kallo ya matsu ya matsu sosai ya auri shaheeda shi kad’ai irin son ta da yake dan’kare a zuciyarsa yana jiran lokacin da Zai amayar dashi.ta zuba a plate ta zauna tana bashi a hankali cikin sigar jan hankali. Mommah ce ta tilasta shatu sai taje dubashi, ta mi’ke tana zun’bura baki a zuciyarta take tunanin ita mommah bata san itace silar ciwon bane ta tabbata yanzu idan taje sai ya huce haushin abinda tayi masa. Hafsa ce cikin fad’a tace “Ba zaki tashi kije ba sai na ‘bata miki rai baki san d’an uwanki bane shi duk duniya baki da kamarsa fa shi da Ammar.” Mi’kewa tayi ta fita niyyarta idan ta fita ta la’be ta dawo tace taje, sai dai a rashin sa’arta Nahna ta mi’ke tace “Bari muje na san halinta yanzu ta ‘buya tace taje.” Ta tura ‘kofar bed room d’in a hankali bayan ta shiga parlourn hakan yasa Nahna saurin juyawa ta koma. Ita kuwa shatu mummunan gamo tayi shaheeda ce a gefen Imran tana ta shafa masa fuska wai tausa take masa ta shige jikinsa sosai kamar me. Da sauri shatu ta runtse ido tayi saurin juyawa shi kuwa Imran motsin da yaji ne yasa shi saurin mi’kewa sai yaga fitar shatu da sauri ya janye jikinsa yana wa shaheeda wani irin kallo “sau nawa zan gaya miki bana son irin wad’annan abubuwan bafa wayewa bace yanzu kinsa yarinya ‘karama ta gammu a haku me kikeso tace mai kike so tayi zargi a zuciyarta?” Shaheeda marairaice masa fuska tayi “Haba habibi meye a cikin hakan kawai fa tausa ne amma tunda baka so insha Allah na daina Allah ya kaimu lokacin da zaka zama halal d’ina in nuna maka pure love da ba surki amma waccen yarinyar mai take zuwa yi har bed room d’inka?” Runtse ido yayi yana tunanin lamarin yarinyar baya ko son ganin fuskarta tsoronta lamarinsa yake bashi don haka dole ya samarwa kansa lafiya ya fita sabgarta kafin tayi abinda zai kaishi lahira burinsa ma lokacin bikinsa yayi ya tattara ya bar gidan ba sai ta ganshi bama balle ta hukunta shi da ‘kazantarta. A ranar Dahda ya dawo amarya aka shiga giringid’ishin kama miji mommah dai ko gurinsa bata jeba balle taga abinda zai ‘bata mata rai, sai da ya gaji da kansa ya shiga part d’inta tana zaune da kwalliyarta ta tsadaddiyar atamfa ta kashe d’auri parlorn nan sai ‘kamshin turaren wuta yake yi. Murmushi ya sakar mata “uwargida ran gida barka da hutawa ni nazo gaisheki tunda ba’a nemansa” murmushin ta saki itama bayan ta gama saurararsa tace “hakan da kayi shine abinda ya kamata ka bi cikakkiyar sunnar manzon Allah ya hanya?” “Alhamdulillah” ya furta yana sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ya tabbata da itace da girki da tuni ta kai masa ruwan wanka ta kuma taimaka masa da tausa da lafiyayyen girkinta tana zuba masa tana murmushi ba dole dijah ta sace zuciyarsa shi kad’ai ya san wacece dijah ya kuma tabbatar ba zai samu kofa kwafinta bane balle wacce ta kaita. “Na biya wajen hajja wai me ya faru ne ta tabbatar min da aljannu a cikin gidannan wai ba zata sake zuwa ba” yana murmushi ya fad’a mommah ma dariyar tayi tace”Ba mamaki da aljannun a d’akin da take sauka amma mu dai bamu ta’ba gani ba” “Ni na sani na san rigimar hajja ce yanzu ba ma wannanba ta rigime min sai anyi bikin Imran nan da wata d’aya da Rabi” mommah ta saki murmushi kafin tace “Masha Allah Allah ya nuna mana me yayi saura ai ya gama gininsa Allah yasa albarka yasa abokiyar arzikinsa ce yana d’akima ba lafiya” Dahda ya mi’ke “ai naje na duba shi ina shigowa zainabu ta fad’a min Allah ya bashi lafiya yace min stress ne yayi masa yawa Imran ne akwai son kud’i baya son hutawa” mommah tana dariya tace “kyan d’a ya gaji ubansa” *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍 NAZEEFAH SABO NASHE FREE📚 08033748387 -15 ***** Tun daga lokacin Imran ya tattara shatu ya watsar a gefe baya shiga shirginta sam ko a waje ya ganta baya zama idan kuwa yana waje tazo da sauri yake barin wajen. Hakan da yake yi kuma sosai ya fara damun zuciyar shatu bata so ba sam bata so ya daina shiga lamarinta ba haka kawai take son ta dinga ganinsa tana jin muryarsa da kuma kyakykyawan murmushinsa, hakan yasa ko da yaushe take zama a main parlour kawai don yas shigo ta ganshi taji’kamshinsa ta kuma ga kyakykyawan takunsa da yake yi tamkar a cikin izza bata san daliliba haka kawai IMRAN AHMAD MANGA yake burgeta. Ba wai soyayya take nufi ba tunda har a lokacin bata san so ba kawai dai burgeta yake tsaftarsa kallonsa tafiyarsa maganarsa komai Imran manga yayi burge shatu yake sosai har cikin zuciyarta ba mamaki hakan yana da ala’ka da zamowarsa d’an uwanta kuma jininta wanda duk duniya bata da na biyunsu. Ganin ya daina shiga shirginta itama ta tattarshi ta watsar ta kama Ammar abinta da uncle d’inta Hisham da kullum suke tare indai suna gidan. Tuni ta mayar da hankalinta akan karatunta both islamic da boko bata wasa burinta ta zama mai ilimi ta kuma iya english kamar yarda taga su Anty hafsa suna yarawa abin yana burgeta yana sata nishad’i, hakan yasa take damun mommah da zancen ita kuma mommah ta dafa kanta tace “sha kuruminki shatun mommah zaki iya turanci da ko bature england sai ya sara miki” hakan da mommah take fad’a shi yake ‘kara mata ho’b’basa taji tana so tana kuma zakwad’i da karsashin son zamowa baturiya mai yara english ba gargada ko tuntu’ben harshe. Sosai take dagewa lamarin har tsoro yake bawa mommah ganin yarda ta mayar da karatu abokinta ko da yaushe zaka sameta da littafi na islamiyya da na boko. Tsoron mommah d’aya kada karatu ya sa ‘kwalwarta ta’buwa don haka sau tari take ‘kwace littafin ta saka mata kallo ko tace tayi barci ko na rabin sa’a ne kwanyarta ta samu hutu. Tuni su hafsa suka tattara suka koma Abuja saboda yawan damunsu da hajiya mama take da yawa akan hutun ya isa, kullum fad’a take tana ‘karawa “ Ba hauka bane abin ku tattaro komatsanku ku dawo nima ina bu’katarku idan bikin yazo kwa koma tunda dai bata da wasu sha’ki’kan da suka wuce ku” hakan yasa dole suka tafi zuciyarsu cike da tausayin mommah ganin yarda kishiya da dangin miji suka sakata gaba. Koda suka gayawa hajiya maa murmushi kawai tayi kafin tace “haka rayuwar ta gada ba yarda bawa zai zauna ‘kalau bai jarrabeka ba idan kaga Allah baya jarrabarka ma ka binciki kanka balle d’iya mace a gidan miji taya kuke zaton zata samu aljanna a ‘bagas ai dole ne a jarrabeta ko ta’bangaren kishiya uwar miji ko dangin miji, ‘ya’yansa ko d’ungurungum mijin ma gaba d’aya babu wata mace da zata ce salin Alin tana rayuwarta ‘kalau tsakanin bawa da ubangiji godiya kawai a duk yanayin da ya tsinci kansa don haka ta godewa Allah tunda mijinta na sonta saura kuma ta barwa Allah ta sha mamakin hukuncinsa ai hukumullahi la ajabun.” ******** Wata d’aya ya rage biki a kuma lokacin ne ‘kannen Ahmad manga mata masu ji da kansu suka iso gidan d’an uwansu da set d’in akwatinan lefe za’a wuce dasu dangin uban shaheeda da suke Abuja. Mamaki ne ya hana momma magana da suka samu a sashenta suka ce taje taga lefen da Imran ya had’a. Baki sake take kallonsu kafin ta furta “shi Imran d’inne ya had’a lefe ba tare da sanina ba saboda bai mayar dani uwa ba ko mai?” Tsaki hameedah tayi tana tauna chewingum sai kuma ta tintsiro d’ankwalinta gaban goshi tana watsawa momman kallon raini tace “yo da ke har wata tsiya kike d’aukan kanki d’a dai kin haifa amma baki isa kice zaki juya shi ba wannan kam sai yarda muka ga dama kin dai juya ubansa mun’kyale ki yanzu kam the table Don haka muka saka dole ya auri shaheeda mu juya shi son ranmu kema ki d’and’ani rad’ad’in da mu kaji da kike juya yaya manga ki taso kiga lefe idan kinga zaki iya idan kuma ba haka ba kya gani a jikin surikarki kuma ‘yar kishiyarki shaheedah.” Ran mommah ne ya ‘baci har ta gagara ‘ko’karta furta ko kalma d’aya ce ga hameedah yarinya ‘yar cikinta da take tsaye take mata fitsara. Suma duka sauran ba wanda bai furta albarkacin bakinsa ba sannan suka juya suka tafi suna dariya da shewa burinsu ya cika sun ‘batawa mommah baiwar Allah zuciya. Tsahon lokaci tana zaune a wajen ta kasa mi’kewa tufka take a ranta kawai da warwara tabbas idan ba’a yi wasa ta bari a kayi aurennan zasu ci galaba a kanta za kuma suyi duk abinda suka ga dama hawan jini suke neman cusa mata da ciwon zuciya,ita bata ga abinda tayi musu a zahirance da bad’inance kawai dai ‘kiyayya ce suke mata su kansu da basu san asalinta ba balle tushenta. Ya zama dole tayiwa tufkar hanci lefe dai ba zata je ta gani ba kuma Imran zai zo ya sameta zata nuna masa ita d’in nan dai itace wacce ta haifeshi ta d’au cikinsa wata tara ta kuma shayar dashi nononta na tsawon watanni sha takwas. Tsawon lokaci mommah na zaune a parlournta ranta a matu’kar ‘bace ta gaji ta gaji da tozartawa da wulakancin dangin miji, mafita kawai take nema tun daga parlournnata tana jiyo su tana jiyo ba’ka’ken maganganu da suke jefo mata masu kama da gugar zana hakan ya ‘kara hassala zuciyarta taji kuma zata iya komai don ‘kwatowa kanta ‘yancinta ciki kuwa har da samowa Imran aure ko da a cikin d’iyoyin friends d’inta zata nuna musu tana da iko da d’anta kuma ba wata shegiya da zata yi mata tin’kaho da d’anta alhali sanda tayi na’kudarsa ko wacce cikinsu tana can shanye da baki tana barci.lokaci yayi da zata farka daga barcin da take ta amshe matsayinta na uwar d’a mai cikakken iko akansa fiye da kowa a duniya. Shigowar shatu ne ya farkar da ita dogon tunanin da ta tafi, shatu da hanzari ta ‘karasa wajenta ta dafa takanta ganinta cikin damuwa, tana son mommah jinta take tamkar innaji don haka sam bata son ‘bacin ranta kuma zata iya gogawa da kowa idan har yace zai shiga gonar mommah.murya can ‘kasa tace “Mommah menene meye ya sameki? Wad’ancan mutanen ne ko?” Momma ta girgiza kai tana janyo shatu jikinta “Bakomai shatu yau naji ina burin dama ke budurwa ce da ma ke kin kai muzalin aure da ba abinda zai hanani aurawa Imran ke da nayi alfahari da haka”shatu ta zaro ido “aure mommah ai nayi ‘karama” Murmushi mommah tayi kafin ta furta “shi yasa a zancena kika ji nace dama, duk da haka ba matsala insha Allah ba zan rasa wacce zan ‘karawa Imran a matsayin mata ta biyu ko da hakan yana nufin za’a yi tashin hankalin da ba’a ta’ba yi ba da wad’ancan mutanen” shatu ta ja ajiyar zuciya tana kallon mommah da hawaye yaso zubo mata ta kuma tabbatar na zallar’bacin raine. A zuciyarta ta ‘kudurce tabbas sai tayi maganin mutanennan a yau kuwa ba sai gobe ba taji itama a zuciyarta dama ita d’in budurwace a aura mata Imran da kuwa tayi sa’a kuma sai taci uban shegiyar shaheedan mai goshi kamar fitilar jirgi dama ta tsaneta tunda sanda ta ganta a kanainaye a jikin Imran. Shigowar Imran ne da ‘kamshin turarensa ya sata kai idonta kansa yayi kyau sosai cikin wani black yard african attire d’inkin zamani bai kai gwiwaba haka nan hannunsa gajerene kuma rigar tad’an kama shi kad’an an yi masa ratsin light brown daga gefen aljihun da kuma rigar ta lura yana son irin kayan yawanci shigarsa kenan yayi kyau sosai duk da kansa ba hula. Bai ko kalli sashen da take ba ya ‘karasa inda mommah take fuskarta a had’e sosai. Zama yayi sosai kusa da ita yana dafa kafad’arta had’e da zubawa shatu harara, kafin ma yayi magana ta mi’ke don ta san ma’anar hararar tasa ta shige bedroom d’inta murya can ‘kasa tace kyau kamar aljanni sai zallar ba’kin hali”. “Please mommah na mai ya faru ne naga fuskarki ba walwala? Kuma su anty fannah sunce kije kiga lefe kin ‘ki why mommah?” Kallonsa tayi kallon cikin ido kallone da tun suna yara suka san tana yi musu idan sunyi mata babban laifi. Da sauri ya rusinar da idonsa baya jurewa wannan kallon baya son sa yana razana shi ya kuma san duk sa’in da mommah tayi shi ranta ya kai ‘kololuwa a ‘baci “ please mommah am sorry duk da ban san laifina ba” “ sorry for what Imran? You are sorry because ka wula’kanta ni ka nunawa duniya bani da amfani a wajenka ka nunawa duniya dani da babu ni you can make decisions about anything aurenka Imran ace sai dai ace nazo naga lefe? Ana yar min da magana baka neman albarkata baka damu da farincikina ba ko da yaushe sai ‘bacin raina nagode kaje ka yi aurenka kaje mutanen da kake tunanin zasu baka farin ciki su baka fiye da wanda ni zan baka Allah ya sanya albarka a aurennaka but put this in your mind bani ba ‘yan uwana a bikinka ba zamu zauna muga ‘baci rai ba.” Daga haka ta mi’ke ta shige d’aki jikin Imran ne yayi sanyi ji yake kamar yace ya fasa baya son ‘bacin ran mahifiyarsa bai san me yasa zuciyarsa ta kasa ha’kura da shaheedah ba, tsawon lokaci yana zaune kafin shatu ta fito tana ‘yar wa’karta ta “uwa tana da girma mahaifiya tai mini komai” da sauri ya kalleta gani yake kamar da shi take da shi d’in kuwa shatu take amma ya kasa ta’buka komai yana juya kalaman wa’kar shatu a zuciyarsa. Ko da ta fita bata zame ko ina ba sai wajen mai gadi, da murmushi y tareta don yana son shatu musamman yarda take girmamashi ga kyauta akai akai “uwata ta kaina ya aka yi?” Ya fad’a yana mata murumushi shatu tayi ‘kasa da muryarta “Baba taimako zaka yi mi please amma bana son kowa ya sani” ya girgiza kai “ shatu danger yau kuma wa ya takaloki?” Dariya tayi kafin murya can ‘kasa tace “wasu ‘kadangarun bariki zanyi magani ga dubu biyu ‘kai’kayi zaka siyo min don Allah” Baba ya ware ido “Aa fa shatu’kai’kayi kuma mai zaki yi dashi?” Ta had’e rai idan ba zaka taimakeni ba shikkenan bara na tafi” ganin tayi fushi yasa yace “zo uwata zan taimakeki ai ba zan’ki mai taimakona ba” ta mi’ka masa kud’in tana dariya.