💫MATAN??? Ko MAZAN???💫 ✍🏻M SHAKUR Chapter 1- FEMINISM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAIJINKAI. Note: Wannan littafin kagaggen labari ne ba rayuwan wata ko wani narubuta ba, is just fiction danai highlighting major issues dake kawo misunderstanding a aure, I hope we all read and learn. 🙏 EPISODE 1️⃣ Zaune suke akan kujerun dake cikin garden din yahuza suya na bayan central mosque. Maza hudu ne, dukansu suna sanye da suit but duk sun ciccire jacket din sun makala jikin kujerun dasuke kai da alamun daga wajen aiki suke, gasassun kaji ne agabansu da shayi sunasha suna kallon katon TV dake wajen inda ake buga kwallo tsakanin Manchaster da chealsea. Kana ganinsu kasan suna bala’in enjoying match din dan sai gardama suke suna dariya kyakyakya. Wayan daga daga cikinsu ne yay kara hakan yasa yakai hannunshi yataba aljihun gaban riganshi batare daya janye idanunshi dagakan TV ba yaciro wayan yajanye kanshi daga TV yakalli screen din ganin Madam yasa yadanyi tsaki ya ijiye wayan yacigaba da ringing sauran mazan dayake zaune dasu suka kalleshi dan yake yayi yakai hannunshi yana shafa kirjinshi yace “Madam ce wlh ke kirana tahanani sukuni” dauke kansu duka sukai daga kallonshi kaman hada baki suka cigaba da kallon match din abinsu. Karfe 11:30 daidai aka gama match din inda Manchester sukaci da 4:2, wanda aka kira dazune yatashi yana daukan wayanshi dake ringing har lokacin da jacket nashi duka ya rike a hannu yace “lemme be on my way, inba hakaba Madam zata kashemini batteryn waya wlh, saida safen ku” daya daga cikin ukun dasuka rage zaune shima yamike dasauri yace “nima gani biye dakai Engineer bazan iya da masifan matan nan this night ba tahanani bacci nima” yana maganan yadauki jacket nashi da car key yabi Engineer dasauri zuwa wajen dasukai parking cars dinsu, sake sallama sukayi kowanne ya shige motarshi suka bar wajen. Daya daga cikin biyun dasuka rage zaune ne yakalli dayan yace “karfe nawa zaka bar nan Nura?” juyawa wanda aka kira da Nura yayi kaman bashi akama magana ba yadaga hannunshi sama yakira daya daga cikin yaran dake aiki a Yahuzan da gudu gayen dayakira yazo cike da girmamawa yace ”yallabai gani” juyawa Nuran yayi yakalli mutumin dake kusadashi yace “ya akaro dakai ko zaka wucene kaima?” girgizamai kai yayi alamun a’a hakan yasa Nuran yajuyo yakalli yaron yace “karo mana shayin goruba da kaza asaka masa aciki da gizzard, kasa yaji separately bancin yaji sosai" wucewa yaron yayi yatafi Nura yadauki wayanshi zai fara tabama Musa yace “wai har yanzu kaida Hadiza baku shiryaba? Kai to kasauke girman kanka ka nemeta kuyi sulhu mana” tabe baki Nura yayi yace “wlh ko zan mutu bazan lallashi yarinyar nan ba cus nagaji, any little misunderstanding wanda daga wajetane fa yake farawa amman kullum nike neman sulhu akan wani dalili? She keep taking advantage of rashin son hayaniya na, yo bansan ciwon kaina bane aka gayamata?” Dasauri Musa yace “haba abokina kaima kasan mata da fish brain biyemata zakayi” dasauri Nura yace “bazaka gane bane, duk yanda zan suffanta maka Hadiza bazaka ganeba, she’s so bossy, tanada mentality dinnan na feminism, gani take dani da ita daidai muke shoulder to shoulder, she feels irin india kinada kudinki babu shit din da namiji zai kawomiki kidauka, you don’t need him for anything, she don’t care about me one bit billahillazi kaman ba aurenta nake ba” dafashi Musa yayi yace “chill please kodan yaranku ku shirya haba, Aman is just 4,5yrs ina, little Amal kuma 2 please banson yara tun suna kanana su taso suna ganin iyayensu basa shiri kaji Nura” kabar da hannunshi daga kafadanshi Nura yayi yace “enough Man, talking to Hadiza is impossible, barni nima nabita nazama fish din but saidai ni bazan zama sardine irinta ba mara hankali dake karewa a gwangwani ba, dan trust me mentality feminism nata nan is taking her nowhere, wlh saina gwadamata bonu duk randa takaini bango yar durun uwa” ya kifo uban ashar da hausan shi haba Musa ya kwashe da dariya, dan dariya Nura yayi shima yace “kaikuma meya faru kaima kabiye mini dayin dare awaje yau dan is obvious kaima da naka guntun matsalan kaima” dan tsaki Musa yayi yana tsaida dariyan dayake yace “matata, kaga Maman Shatu I don’t even know idan mace ce ita dan at this point cewa nake anya ba namiji bace itaba kuwa” dan dariya Nura yayi daidai lokacin ana kawo musu ordersu yaron ya ijiye yawuce yatafi, tsiyaya musu shayin Musa yayi yadauki kopin yakai baki yadan kurba ya tsaya kaman mai tunani yace “Bro imagine fa duka duka yanzu fa na shiga 45yrs amman this woman na neman maidani tsohon dole, she hates anything tarayya dani, dazaran nazo saita fara ni bansan yakamata yanzu na soma rage kwanciyan aure da itaba nasomas tsufa, menene menene, wai is high time mufara hakura dayi yara sun girma, Shatu is 16 zata shiga university next month let’s just focus on yaranmu, I was like what da hell! An gayamata ni katako ne ko sotake da tsufana nafara sopy”? Bushewa da dariya Nura yayi harsaida ya yarda naman bakinshi kasa yana nema ya kware, Musa yace “kadaina dariya is a serious matter ni da kai munada banbanci, kai daman bakin zuciyanka da girman kanka bazai barka kanemi Hadiza ba I don’t even know yanda kake surviving wlh, niko bazan iyaba kullum da rokon Allah nake hada matan nan kafin tabari indan taba, da girmana da darajata Maman Shatu ta maidani maibara shine fa jiya tamini karatun Alam Nashara matan nan atafaufau tahanani wai munada budurwa mudaina yi” dariyan da Nura keyi saida yan wasu table suka juyo suna kallonsu dasauri yarage sautin dariyan, kwana nawa kenan kullum cikin kunci yake but yau Musa nabashi dariya sosai wlh he’s so funny and hausan shi is just everything, dole ma kai understanding pains nashi sabida kalamomin dayake using to express it, tsagaita dariyan yayi yadauki nama yakai baki yace “to be honest with you Musa bawai banson nasami natsuwa bane ina so sosai but halinta is making me loose interest and love for her, banmason in tuntubeta da neman kwanciyan aure, itakuma ko oho bata damu dani ba, she no send me fa” cike da takaici Musa yace “I don’t know yaya brain din mata ke aiki imagine fa sun mana laifi but idan sun taru cikinsu they will belike mijina yamin kaza kaza kaza kaga ana kaimu online ana please hide my ID akai karanka amman baza su taba fadin suga kaza kaza da sukema mazajensu ba bunch of hypocrites, masu fuska biyu kawai, banda gayu da nunama kawayensu suna more mazajensu da aurensu babu abinda suka iya, ita kuma dama nafada mata idan bata chanza ba wlh she is on her own, daleliyar kishiya zanyo mata, da kudina da sana’ata wlh bama saina nemi mata ba Gwaggo zan kira a kano asamomin yarinya yar achan achan atoh ni wlh ban tsufaba garau nake, anma kawomin wasu magungunan basir daga Cotonou bazaka sha ba”? Girgixa kai Nura yayi yace “kaidai da shaye shayen magungunan basir din nan” dariya Musa yayi yace “kaima yakamata kasha wlh ya wanke maka mara tastas, fire for fire wlh ka lallasa Hadiza” “inaaa ni bazan biyemaka ba narasa ina zansa kaina, baridai maybe idan komi ya daidaita nazo na amsa”. Wuraren 1.30AM sukatashi Nura yabiya kudin komi, kowanensu yashiga mota dan tafiya gida, Musa yace “zakazo office kaduba motocin ne gobe sun iso fa” Gyadamai kai Nura yayi yace “inada wani important meeting gobe but zan shigo dazaran nagama” Musa yace “to shikenan nimafa sonake nazo naga site dinnan, terrace dinnan yamin kyau dakukayi” “ba kaki sayaba bakano da son kudi” ckin dariya sosai da barkwanci Musa yace “shikuma bazamfare annubazaranci da kudi, nabiye maka saika karan mini da dan jarin motoci na” dariya dukansu sukai sukai sallama kowa yaja motanshi sukabar wajen. Kinason magana dani M shakur??? Chat me up by clicking on this link wa.me/+2347012181461 Parking yayi agaban wani babban gida wajajen 2 nadare. Sauka yayi yana kallon wata sabuwar red 2024 Toyota grand highlander dake pake akofar gidan duka duka last month ya chanza mata mota 2023 Toyota Camry hybrid wato bai mataba shine maybe ta saida tasayo wani, dan murmushi yayi yawuce yana ciro key dinshi yabude kofan yashiga ciki yamaida kofan yarufe yajuyo yakunna wuta lafiyayyen hadadden classic falo ne, ijiye key yayi kan tray dasuke ijiye key yaduka yacire covershoe kafanshi yasake juyowa yabi falon da kallo dayake tsaf tsaf banda motan Aman dake kan kujera hannu yasa yakashe wuta sannan yawuce yahau stairs harya fara tafiya yaji kukan Amal chak ya tsaya cus badaga sama yakejin kukan nan ba and dakin Amal na upstairs, shiru yayi jin magana kasa kasa. “sorry Amalulu, Amalilin Mommy, Amalilin Aman, Amalulu na Amalulu yar lukuta, kiyi bacci zakiji sauki gobe kinji, zazzabi ne saina zane zazzabin nan dake damun mini yarinya na” muryan Amal yaji tafashe da kuka sosai cikin muryan yara tace “Momyyy” dasauri yajuyo yashiga saukowa daga staircase direct hanyar dakin yar aikinsu yayi dake kusada store room na gidan, tsayawa yayi gaban dakin yasa hannu yakunna wutan wajen sannan yayi knocking kofan tareda bude kofa atare dasauri sabida yanda yakejin kukan Amal, wata yar budurwa ce doguwa tsaye tagoya yar yarinya dabazata wuce 2yrs ba abayanta, wata yar karaman katifa ne adakin ta yan boarding sai ganamasgo saikuma kwalayen magunguna da flask na ruwan zafi da gwangwanin cerelac da bowl da spoon duka akasan dakin, adan tsorace yar budurwan ta duka kasa goye da Amal abayanta ganin maigidan dabai taba zuwa nan ba tace “ina yini” gabanta na faduwa dan yaune rana da farko da Baban su Amal yataba zuwa wajen nan, sosai yake kallonta baima tsaya amsa gaisuwanta ba yace “me Amal keyi anan da daddaren nan”? Tana duke akasan still jijjiga Amal dake kuka take abayanta tace “batada lafiyane Alhaji” “Mamanta fa”? Dasauri tace “Anty tadawo daga aiki tagaji bacci zatayi” ranshi abace yace “ita tace ki kawota nan dakin”? Gyadamai kai tayi batare data kalleshi ba tace “eh” “bani ita nan” batai musa ba tashiga kwanto Amal dasauri, yarinyar was looking so weak sai kuka take ta yarda zanin tadauketa ta taso ta taho har inda yake tsaye agaban dakin takawomai ita, itama Amal tana ganin babanta takara fashewa da kuka tace “Daddy” zafin dayaji ajikinta saida yadan firgita ya rungume yarinyar da sauri ajikinshi yace “my princess” yakalli yar aikin dahar takara dukawa anan gabanshi yace “wani magani tasha”? Dasauri tace “Anty tace nabata wayanchan”? Tanunamai magungunan dake gaban katifar ta, Ibuprofen suspension ne dakuma Tuxil D na mura da tari, jiyayi ranshi na tafasa dan yaranshi are his life, cikeda takaici yace “how many mil ma kika bata? Tun yaushe take wajenki”? Dasauri tace “tun wajajen 9 Anty takawomin ita, cikin marfi Anty tace nababbata zatai bacci” “maisa baki kaita da jikinta yayi zafi haka ba akaita asibiti tun 9 har 2 nadare” kanta na kasa still da zuciya daya tace “Anty tace karna kawota bacci zatayi tagaji ta kwana awajena” kallon yar aikin yayi takaici yasa kawai yajuya yawuce yahau staircase rikeda Amal dake kuka sosai ajikinshi, direct dakin Maman yawuce bude kofan yayi kai tsaye yasa hannu ya kunna wutan dakin, wata kyakkywan faran mata ne kwance kan wani makeken lafiyayyen gado tarufa dawani beautiful bargo AC na aiki dan dakin sanyi tana bacci mai dadi, wucewa yayi gaban gadon ya bubbuga filon da kanta kekai yace “Hadiza, Hadiza” firgigit tabude idanunta dasukai ja cikin bacci tabishi da kallo tana mika tana kallon Amal dake kuka sosai tana miko hannu kaman zata kamata, cikin muryan bacci tace “Nuri lafiya zaka kawomin Amal ina bacci batana wajen Ummi yar aikinmu ba pls kamaidata I need to sleep na bala’in gaji wlh” tai maganan tana hamma zata kara jan bargo azuciye Nura ya fizge bargon ya yaye yace “wai what’s is your problem Hadiza? Kinyi neglecting your responsibilities towards me yanzu ma yarana wulakanta mini su zakiyi, this girl is sick baki kaita asibiti ba, baki kirani kin sanar dani ba, kin barma yar aiki ita da magungunan acika marfin idan tai overdosing yarinyar nan fa”? Hamma Hadiza tasakeyi tarufe bakinta sannan tadan yunkuro kadan takalleshi tace “look Nuri banda lokacin fada dakai yanzu Allah ma yasan I don’t have time, dare mahutan bawa ka maidama Ummi yarinyar nan tasan yanda zata kula da ita, she’s great da yara bakaga duk cikin yan aikin danayi tafi dadewa ba almost a year take nema yanzu agidan nan, and my children loves her sosai” wani kalan kallonta Nura yake yace “da ace bani nakaiki asibiti kika haifi yaran nan ba danace banaki bane Amal is just 2 she’s sick crying for you jibi yanda take kuka take miko hannu ki dauketa kina cewa akaima yar aiki, what kind of woman are you da bakijin tausayin yaranki”? “oooohhhhhhhh! Ohh-ho-hooo!” Hadiza tabuga uban ihu tana daura duka hannayenta saman kanta irin ta shiga uku din nan, cikeda gajiya tace “wai all this while so kake muyi fada naki biyemaka cus am busy da work dina baka gabana what’s the meaning na zuwa tashina tsakar daren nan kana neman bala’i na eh? Nace ka maidama Ummi yar aikina Amal for Godsake this is her job we pay for it ba kyauta take mana ba, idan bazaka maidata ba I can call her da wayana tazo sama ta dauketa sutafi, please pls banson problem Nuri, banso, just get out of my room pls katafi dakinka, haa’a kawai katasheni tsakar daren nan da bala’in ka wannan wani kalan neman rashin zaman lafiya ne iyye? Pls kafitan mini daga dakina nace and nagaji nadawo daga aiki ka maidama Ummi Amal she’s good with kids zatasa yarinyar nan bacci pls go away from here” kawai tsayawa Nura yayi yana kallon Hadiza yanda take magana zaka dauka itane mai gidan nan ko itane take putting food on the plate jibi yanda take cemai yafitan mata daga daki kaman itace ke aurenshi ba shi ke aurenta ba, ganin ya tsaya kallonta yake yana jijjiga Amal dake kuka sosai barinma yanda taga Mommy ta na masifa yasa ta buga tsaki. “Mtswwww, kada Allah yasa kafitan nina barmaka dakin, kajika da ruwa kasha” ta tashi fuuu azuciye tasauka daga gadon tawuce tafita daga dakin tana mita, yana ji tashiga wani daki ta bugo kofan tarufe tana murza key jiyayi kaman an dauramai dutse a kirji kallon Amal dake ihun kuka yayi tana kokarin sauka daga hannunshi tana kallon kofa tana mika hannu tanaso tabi mamanta Ya jijjigata yace “sorry Amal, Daddy’s princess stop crying, muje” wucewa yayi yafita daga dakin dakinshi yaje da ita ya ijiyeta kan gado yawuce bayi yatara ruwa yadawo kayan jikinta yacire mata da pampers yadauketa zuwa bayi wanka yamata tsaf kana ganin yanda yake kasan mutum ne mai tsananin son yara fito da ita yayi daure a towel yawuce yafita yaje dakinta hadadden daki komi pink ga zane komi organize wani shimi yadauko yasamata da pampers yace “zakisha tea Princess”? Girgizamai kai tayi a’a, yace “juice, cheese balls, rice, omelette” gyadamai kai tayi dasauri daya fadi omelette hakan yasa yadauketa sukaje kasa ya kunna wutan falo ya shiga kitchen da ita baimasan ta yanda zai fara mata omelette dinba, tsaki yayi yafito yaje gaban dakin yar aikin yayi knocking bude kofan tayi adan taushashe yace “danzo ki soyama Amal kwai” Amal na ganinta tamika mata hannu dan tadauketa dasauri Nura yace “wait Princess aiki zatayi” dasauri yar aikin Ummi tace “ai na iya aiki ina dauke da ita kawota” dan kallonta yayi sai kawai yabata Amal din ta karbeta tana murmushi ya matsa gefe fitowa tayi tana tafiya tana kallon fuskan Amal tace “namiki omu omu”? Dasauri Amal ta gyada mata kai tace “omu omu” Ummi tace “to muje namiki mai dadi ko”? Amal tasake jinjina mata kai. 💫 MATAN??? Ko MAZAN???💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣ Binsu da kallo Nura yayi yadan sauke ijiyan zuciya koba komi tayi shiru yanzu, komawa falo yayi yakunna wuta yazauna kan kujera, yadawo ko chanza kaya baiyiba, bai wanka ba ranshi yabaci, kunna tv yayi yana kallon news dudda hankalinshi bawai yana wajen bane dan damuwa ne cike fal aranshi. Yana zaune awajen Amal tafito da kanta rikeda karamin bowl da aka soya kwai mai kyau aciki tace “Daddyyyy Oumu Oumu” tana nunamai bowl din, dan murmushi yayi tazo kusada shi daukanta yayi yazaunar da ita saman kujera kusadashi tahauci, ruwa Ummi tabiyota dashi a water bottle nata mai kyau ta ijiye agabanta takoma chan nesa dasu wajen dinning tazauna akasa duk atakure take dan batama saba ganin mai gidan ba, kusan 1yr tana aiki agidan itada yaran sukafi zama agidan nan, sai yau ne take ganinshi hakan yasa duk takejinta atakure. Dauke kanshi Nura yayi dagakan tv ya kalleta yanda tazauna akasa kaman wata mara daraja irin yar maulan nan dukta takure tana wasa da hannunta bini bini tana kallon Amal dakecin kwai abinta da hannu kusada shi yasa yadanji wani iri, he always hate yan aiki to be honest yaune rana ma na farko daya taba kallo fuskan yarinyar nan dake musu aiki agida kuma this is almost 1yr take gidan nan, ba yabo ba fallasa yace “jeki kwanta kiyi bacci” kanta akasa cikeda respect tace “saita gama cin abinci na wanke mata hannu na gyara wajen nasata bacci tukunna zan iya bacci” dan jinjina kai yayi saikuma yayi shiru bai kara cewa komiba, yakai hannunshi yataba wuyan Amal din jikinta yadan rage zafi maybe sabida ruwan daya watsa mata neyamaida idanunshi kan TV, tass Amal tacinye kwan ta cillar da plate kasa tace “akoshi” dasauri Ummi ta taho ta duka tadauki plate din da cokalin adan kunyace dan she’s not comfortable yanda Baban ke wajen tamika mata hannu tace “zo aje a wanke hannu” makemata kafada Amal tayi zata kama Babanta da hannun kwai dasauri ya matsa yace “je princess awanke miki hannu” turo baki tayi takalli Ummi dake kallonta, cikeda dabara da iya wasa da yara tace “zomuje muyi wasa da pampoo akitchen” wani kalan dirkowa Amal tayi abin harsaida yabama Baban mamaki tazo gaban Ummi da dugudu tace “ruwaaa, pampoo” da sauri Ummi taduka ta dauketa tana murmushi tace “yauwa Amalulu na muje, idan Aman yatashi gobe shima mu soyamai Omu Omu ko”? Gyadamata kai Amal tayi sukatafi kitchen, dan ijiyan zuciya yasauke to some extend kam she’s good with kids kawaidai shi bayason yan aiki ne and he don’t trust hygiene dinsu, dan ijiyan zuciya kuma yasauke idan ba yan aikin ba yasan Hadiza ba aikin nan zatayi ba ko sama da kasa zata hade. Tass ta wanke mata hannu ta share mata baki tare suka wanke plate da spoon din tace “yanzu sai bacci ko, nagoyaki”? Gyadamata kai Amal tayi Ummi ta duka tace “yauwa babuuu Amalily” da gudu tahau bayanta tana murna dariya tayi bataso tasake fitowa daga kitchen din hakan yasa sai kawai tacire dankwalin kanta ta warware ta goyata dashi, wasu manya manyan kitson hannu ne akanta shiku ya tsufa sosai amman tanada bakin gashi mai kyau da santsi, zagaye kitchen din tashigayi da ita tana jijjigata tana mata waka ahankali. “Amal Amal yar gayu, Amal yar kyakkyawa, Amal yar fara saidai tana fitsari agado” dan ihu kadan Amal tayi tana hamma Ummi tai dariya tace “to nadaina Amal bata fitsari agado, Amal jaruma ce gimbiya mai kafafun zinare yi bacci to” haka tadinga jijjigata tana zagaye katon kitchen din nan da ita dantai bacci. Gajiya yayi da zama afalo dan dama jira yake agama wanke mata hannu yadauketa suje sama gashi kusan 30min shiru basu fito daga kitchen ba, baki yabude zai kwalama Yarinyar kira yakasa, shi wlh ya manta sunanta kuma is somehow yakirata yar aiki, dan tsaki yayi yamike tareda kashe tv yatafi wajen kitchen din, kofan abude hangota yayi tana tafiya a kitchen din tana jijjiga Amal data fara bacci abayanta suna zagaye, ko kadan bata luradashi ba dan bekai gaban kitchen dinba, yanda yaga take zagaye take jijjiga Amal abayanta gently tapping her bombom ta saman zanin goyo tana mata wake haka sai kawai hakanan yaji yaji wani iri aranshi, he can’t even understand idan guilt yakeji ko anger, wannan wani kalan rayuwane ace mahaifiyar Yarinyar na bacci anbar yar aiki da yarinya bata runtsaba tsakar dare, tun 9 yanzu kusan 3 idanunta biyu, is she not human being ita? Ko machine ce? Kowa fa deserves this sleep, dare mahutan bawa, koda aikinta ne there’s nothing bad idan Maman yarinyar natare dasu to help her out, abin is really really somehow azuciyanshi, jiyayi ranshi yamai badadi dauke kai yayi tareda dan gyaran murya batare daya karasa kitchen dinba, dasauri Ummi tajuyo jin gyaran murya, batare daya kalli kitchen dinba yace “kawota taje ta kwanta” dasauri Ummi tace “to” goyon tashiga kwancewa kafin ta sauketa tafara jan dan kwalinta ta jefa akanta sannan ta dauketa a hannu tariga tai bacci ta taho ahankali har zuwa gabanshi tamikamai ita tace “gata Alaji” dan juyowa yayi yakalleta ahankali yasa hannunshi ya karbeta yace “sannu da kokari, jeki huta kema” “to” ta amsa tana tsaye awajen, wucewa yayi itama tawuce falo takashe wuta sannan takoma dakinta ko 1min bata karaba sai bacci. ** Wuraren 5 yabude ido sabida zafin jikin Amal data kwana dakinshi, tashi yayi zaune yakai hannunshi yatabata yarinyar nan needs hospital wucewa yayi yashiga bayi ya watsa ruwa yafito daure da alwala yawuce yasauka kasa motsi dayaji a kitchen yasa yawuce kitchen yar aikin yagani tana sharara da goge goge jin knocking kofa yasa ta dago kanta dasauri ganinshi yasa ta duka tace “ina kwana Alhaji” juyawa yayi yace “lpy lau kibar aikin nan kije ki shirya Amal ina dawowa daga masallaci zamu kaita asibiti” bai tsaya jiran amsanta ba yawuce, wanke hannunta tayi ta tafi sama azuciyanta tace Allah sarki Amal dina, dakinta taje ganin bata ciki yasa ta tafi dakin Aman yana baccin shi shikadai batanan to ko dakin Maman take bude dakin tayi da sallama bata wajen hakan yasa tai tunanin dakin Baban, idan da sabo tasaba shiga dan ita ke gyara dakin ta wanke bayi, bude kofa dakin tayi tadauki Amal dake bacci tawuce dakinta wanka tamata ta shiryata tsaf itama tai salla nan da nan tai parking jaka taje kitchen agurguje tamata air frying chips da sausage tasa mata a cute flask nata da ruwa tahada komi da yaro ke bukata, itama taje ta chanza kaya zuwa wani dan dogon Riga baki ba laifi yanada kyau but irin outdated one din nanne shima Anty tabata ta yana gyalen akai tazauna a falo rikeda Amal da yanzu bamata da karfi, shigowa yayi gidan ganinta zaune akasa afalo rikeda Amal data shiryata tsaf in this short time yasa yace “let’s go” dan kallonshi tayi saikuma ta tashi da sauri, harya zauna agaban mota yaga tafito ta kinkimo Amal da katon jakan a hannu tana tafiya da kyar kaman zata fadi yasa kawai yafito yataho da sauri, tsayawa Ummi tayi gabanta nafaduwa ganin yanda ya dumfarota, hannunshi yamika mata yace “bani jakan” bashi tayi yajuya itama tabishi bude bayan motan yayi ya ijiye jakan ya tsaya yana jiranta tana tahowa tashiga baya rikeda Amal saida tai settling down yamaida kofan yarufe yakoma gaba yashiga yatada motan yaja duk wani motsi da Amal zatayi saita tambayeta menene, ciwo, zafi, me kikeso, zakisha ruwa sannu ko Amal dina abinda baitaba ganin Mamanta tayiba. Wani babban asibiti suka tafi wannan karan shiya sauko yabude musu baya da kanshi yadauki jakan yabar mata Amal dayaga tai lakur ajikinta suna shiga aka karbesu sukai ciki office na Dr suka shiga, wani baturen Dr ne yace “meke damunta”? Kallon Ummi Nura yayi yace “meke damunta” ahankali tace “zazzabi take tun kwana biyu bata iyacin abinci, but nafada ma Anty tadubata tace chanjin yanayi ne, jiya tanata tari sai zazzabi, kuma idan tashiga flowers na gidanmu jikinta na kaikayi, idanunta namata kaikayi shima, jiya batai bacci ba kagani kuma yanzu batada karfi ko kadan” tanuna Amal dake jikinta kaman zatai kuka, sosai Nura ke kallonta saikuma yadauke kai yama Dr bayani da turenci Dr yace “za’a basu gado cus tana running temprature da yawa kafin a debi jininta aga meke damunta, tashi yayi zai debi jininta da sabuwan alluran daya bude dasauri Ummi takalli alluran tadan kankame Amal ajikinta, ahankali Nura dake lurada ita yamika mata hannu yace “kawota” batai musu ba bashi Amal tayi Dr yadebi jininta hawaye taruwa yayi a idanunta yabda Amal ke kuka nan da nan aka kwantar dasu awani private room sai kuka Amal take tana mikama Ummi hannu, kasa zuwa Ummi tayi ganin Babanta natare da ita tashi Nura yayi yakalli Ummi yace “zo ketake nema” kaman jira take dasauri taje rungume Amal Ummi tayi tace “likitan nan ko saimun kaishi wajen police yama Amal allura da zafi”? Gyadamata kai Amal tayi a shagwabe, Ummi tace “sannu ko, zakisha Capri ri”? Dan yatsine fuska Nura yayi irin menene Capri ri kuma, Gyadamata kai Amal tayi, dasauri Ummi tabude jaka tadauko caprisone tace “tadaaaaa” wani kalan murmushi Amal tayi dashi kanshi Nura saida yayi murmushin yadan tabe baki yaciro wayanshi aranshi yace “omelette Omu Omu, Caprisone kuma Capri ri ikon Allah” tana cikin bata juice din wayanta dake pocket din jakan kayan Amal yashiga ringing da sauri tasa hannunta daya taciro wata screen touch Vivo ne dataji jiki sosai ganin Anty yasa ta amsa takai wayan kunnenta cikeda girmamawa tace “Hello Anty ina kwana” daga ta dayan bangaren Hadiza tace “kina ina Aman yatashi”? Cikin kwantacciyan murya tace “Uhmm Anty munzo asibiti da Amal ne, jikinta ya rikice” Hadiza najin haka tasan mijinta ne yakawosu asibitin cikeda masifa tace “to yanzu wazai yima Aman brush da wanka yabashi breakfast eh? Ko nine danake shirin fita aiki yanzu zan tsaya nayi all of this, maza maza ki bar Amal wajen Babanta ki kira bolt yazo ya maidoki gida ai nakoya miki yanda ake yin bolt dan nasan nace kifita kije kibi mota along bacewa zakiyi babu inda kika sani, maza maza kira bolt and come back home kima Aman wanka kibashi breakfast ki shiryashi yatafi school kafin school bus yazo keko school bus yazo idan sun tafi ki kira bolt ki kaishi school din dakanki, kina jina tunda ke mahaukaciya ce dakikiya yar kauye dayace kizo kutafi asibiti bazaki iya gayamai zakiyi aiki ba kika bishi, nabaki 3min karki bari su cika ban ganki agidan nan ba, sabida jakanci da dakikanci irin na yan kauye ina biyanki danki kulamin da yara da gida akanme zaki wani asibiti bayan babanta natare da ita, idan kinsan kin gaji da aikin ne bazaki iyaba ki gayamin na sallameki wata tazo ha’aa nida kudi na ko yan aiki guda dari nakeso zan samesu wlh yau yau din nan, zan koreki wlh kika batamin rai” da sauri Ummi tace “kiyakuri Ant……” dip ta katse wayan tashi Ummi tayi dasauri tace “ina zuwa Amal” tajuya dasauri hada ido tayi da Nura dake kallonta hakan yasa da sauri ta tsugunna daganan wajen gado tace “Alhaji zanje gida Anty tace nabar Amal awajenka zanje in shirya Aman yatafi school” kai tsaye yace “koma ki zauna bazaki ba” dasauri ta kalleshi ganin yacigaba da danna wayanshi yasa takoma ta zauna ahankali but gabanta sai faduwa yake kusan 4min da gama wayan wayanta yahau ruri hannu yamika mata yace “bani wayan” daukan wayan tayi tazo har gabanshi ta duka tabashi wani iri wayan yamai a hannu screen din dukya faffashe wannan ai zai iya yagamai fatan kunne saida wayan yakatse yay dialing number ta da wayanshi yatashi tareda ijiye wayanta kan kujera yawuce yafita dan baiso wani yanajin wayanshi da ita waje yafita wajen parking space daidai ta amsa wayan kafinma yayi magana cikin fushi da ihu tace “sabida kaike biyan salary nata kahanata zuwa ko to daga this month kadaina nizan dinga biyan salary nata lemme be in charge of her nai controlling nata to my satisfaction Alhamdulillah inada kudina, but akan mema zaka hanata dawowa ga Aman ko brush baiyiba bai wanka ba yana kuka yunwa yakeji kuma kasan zan tafi shagona yanzun nan maisa kakemin haka? What kind of man are you? Why do u always look for opportunity to belittle me kanunama kowa banda power over anything in our house eh? What is your problem dani? Bakin ciki kake inada kudi kafison kullum ina kasanka ina rokonka do this for me do that for me”? Shiru Nura yayi saikawai yaciro wayan daga kunnenshi ya katse wayan dan talking to Hadiza is impossible, ita ko kunya bataji ta haifi yara saidai wasu su tayata kula da yaran, gatada baki kaman reza talking to her is just too impossible dukan motanshi yayi ya jingina da motan yayi shiru is this how life zai cigaba da tafiyan mai? Bayagane gaba balle bayan Hadiza, ance communication is a key in Marraige but communicating da Hadiza is impossible kafin kayi magana daya tal tayi dari da hamsin, babu one single abu datakemai na mata, she doesn’t take care for him, karma aje batun girki he can’t even remember the last time da Hadiza tadau ruwa ruwan nan dai bottle water tabashi yasha, he can’t even remember wen was the last time yaci abinci agidanshi, shi bayacin abincin yan aiki itakuma batayi saidai kullum yaci abinci awaje ko agidan abokai, tun yana korafi yan aiki na shigo mishi daki harya dena dan yagane idan basu gyaraba dakinshi baza’a taba gyaramai ba, he can’t remember the last time data gaidashi, is as if he doesn’t exit awajenta whenever he tries to talk to her tace yafara fitina da bala’in da korafin da mita shi yabarta tagaji, she’s not remorseful akan abubuwan datake she feels itadashi equal right sukedashi sabida tana matanshi he can’t step and match her ko control her, sabida tana mace doesn’t mean zata kwantarmai dakai that’s just her mentality, Hadiza is very stubborn ga baki Ya Allah, wlh yagaji baison mata biyu dan ko daya bakar wahala take bashi aduniya, baison broken home dan yataso Mamanshi bata tare da babanshi he don’t want that ma yaranshi, baison neman matan banza abinda baiyiba yana yaro shine yanzu zai fara when he’s approaching 50 haba bazai tabayiba but he’s just tired yarasa ta ina zaibi ya gyarama Hadiza zama ya gwada zama waje yakai 1-2 nadare amman ko ajikinta yadawo ma tai bacci abinta he’s just soo tired of everything he’s not happy in his home. Wajajen 10 aka sallamesu da magunguna a hannu suka dawo tunkafin sukai gate na estate dinsu ya hango Aman dinshi kan kujeran security da pajamas ajikinshi da ledan popcorn idanunshi sunyi jaa, jiyayi zuciyanshi takama da wuta parking yayi yafito dasauri security dayake zaune kusada shi yace “Yallabai barka da dawowa Madam ta ijiyeshi anan gashinan yanata kuka yace yunwa yakeji shine na saya mishi Popcorn yamai jiki”? Sabida yanda ran Nura ke daci gyadamai kai yayi Aman yarike hannunshi yakalli fuskan Baban kaman zaiyi kuka gwanin ban tausayi, kaman dan maraya yace “Daddy where’s Anty Ummi am hungry she’s the only one that gives me food and play with me, Mommy never gives me food or play with me” suppressing anger dinshi yayi yaduka ahankali ya shafa kan yaron yace “muje Anty Ummi na bayan mota da princess don’t cry again okay”murmushi yayi yay bayan mota da gudu yabude yashige shikuma ya tsaya yama security godiya tareda bashi kudi sannan yazo yabude gaban mota yashiga ya zauna yaja mota ta glass na gaba yake kallonsu duka yaran sun kankame Ummi suna hira da ita, sai biye musu take kaman yarinya itama, wlh zaka dauka itane mahaifiyar yaran kawai dan ita black beauty ne yaran kuma fararene tas su kaman turawa amman kana ganinsu kaga strong affection tsakaninsu, sunma manta dashi a motan sai hira suke Aman yarike Ummi gam yanata zuba kaman bashi yayi kaman orphan dazuba, akofar gida yayi parking duk suka sauko tana rikeda Amal, Aman shima yarike mata hannu suka wuce ciki yabisu da kallo direct kitchen suka wuce zaunar dasu Ummi tayi kan kujerunsu dake kitchen din dake gaban island, tashiga yimusu girki agurguje dan Aman yunwa yakeji tana attending to them, ta dafa lafiyayyen taliya na manza fevorite dinsu da kaza ta zuzzuba musu a plate tajuye sauran kuma a kula mai kyau takai dinning ta ijiye sannan takoma kitchen tana bama Amal abaki dantaci da kyau, koda yashigo gidan dan tuntuni yana waya awaje kamshi ne yamai sallama wani kalan yunwa yaji yanaji dinning yaje yazauna kaman wanda ke tsoron wani abu bude kulan yayi daidai Ummi tafito da tray na ruwa da fresh juice a hannu dantaji zuwanshi ta ijiye kan dinning taduka tace “ko adafa wani abune daban Alhaji” girgixa mata kai yayi yace “a’a wannan yayi” tashi tayi takoma kitchen, kaman mai tsoro yadau fork yasa yadebo kadan yakai bakinshi yatauna dadin dayaji wlh saida kunnenshi yayi siiiii, baisan sanda yadauki plate yadeba ba shi arayuwan shi yanason home made food rashi yasa almost few restaurants ne baisaniba a Abuja ba yaune rana na farko dayaci abincin yar aiki and wlh yamai dadi sosai tass yacinye yatashi ga mamakinshi rawa yaga tanama Amal tana kai abinci bakinta da wayau dantaci, ga magani dayaga ta fito dasu ta zuzzuba a marfi dan an fadamata yanda zata bata asibiti, shima Aman yataso yana tayata rawan sunama Amal rawa dukansu biyun tana dariya sosai fa tana karban abincin tabata maganin ta shanye tass ba gardama ko kakarin amai suna mata waka Aman na tafi kaman suna studio, jinshi kawai yayi yana murmushi ance some yan aiki suna faking love ko sabida parents na yaran but shi all he sees ana is genuine love, kuma yaran loves her suma dearly hakanan samin kanshi yayi yana kallon Ummi sosai, yarinyar black beauty ce tanada tsayi akalla zatai 23 ko 24, yar kauye ce from her dressing but she’s kind and tanason yaran shi kuma her smile is contagious dan gashi shima yanata yi, sannan the way she dance is annoyingly cute, kaman Ummi taji ana kallonta juyowa tayi da fuskanta ta kallo falon karaf suka hada ido da Nura dake kallonta tana rawa ma Amal. Wanna talk to me about something??? Chat me up anan; wa.me/+2347012181461 MATAN??? Ko MAZAN???💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣ BONUS💃 Sosai kirjinta yabuga da sauri ta sauke hannayenta kasa tadaina rawan tasauke kanta kasa shima daga kallonshi gabanta nafaduwa dumdumdum. Wucewa Nura yayi dasauri sama zuwa dakinshi yakasa daina ganin fuskan Ummi dana yaranshi how happy all of them were, yanda itada Aman kema Amal rawa, bayi yafada dasauri ya watso ruwa yafito yashiga shiryawa dan yafita meeting din dayake dashi is by 2, cream yadauka zai shafa saikuma ya tsaya maisa ya kalleta haka smiling ya tambayi kanshi? He was lost dayana kallonta, yar aikinsu ce fa but he was finding all abubuwan datakeyima yaranshi super cute, dan ijiyan zuciya yasauke saikuma yacigaba da shafaman. Ummi daduk takasa natsuwa itama a kitchen ta tambayi kanta maisa yake kallonta, tun yaushe Alhaji yaganota tana rawa haka? Duk wani kalan kunya kunya da nauyi nauyi taji tanaji, IPad din Aman tadauko ta kunnamusu anan kitchen din dan bazata rabu dasu ba tashiga gyaran gidan duka tanaso tana gamawa tamusu wanka, itama taje tayi saita daura abincin dare. Shiryawa yashigayi cikin suit dan dawasu representative na China company zai hadu dasu yanaso yabasu contract nayin titin cikin estate dayakeyi, yana cikin daura agogo wayanshi yahau ringing kallon wayan yayi ganin Sis yasa yakai hannunshi ya danna call din batare daya daga wayanba yacigaba da saka agogo daga ta dayan bangaren akace “Ya Nura ina yini” “how are you Aminatu ya jikin Hajiya kunje asibitin”? Kasa magana tayi sai bakinta yahau rawa, dasauri yasa hannunshi yadauki wayan gabanshi ya mugun fadi yakai wayan kunnenshi dasauri yace “what happen jikin Hajiya ne meya faru?” Cikin kuka tace “dazun nan tafadi abayi yanzu haka muna asibiti” bugawa kirjinshi yahauyi sosai anatse yace “Dr Tanimu ne ke ganinku”? Dasauri tace “eh shine” dan ijiyan zuciya yasauke yace “daina kuka ya isa babu abinda zai sami Hajiya kinji” kaman yana gabanta gyadamai kai tayi, cikin dan taushin murya yace “is okay, zanyi magana da Tanimu I think zan muku booking flight gobe kutaho nan Abuja taje babban asibiti anan don’t cry again hankalinta zai tashi, akwai kudi awajenki”? Dasauri tace “eh akwai” ahankali yace “to stop crying bari nai magana da Dr Tanimu” nan da nan ya katse wayan yakira Dr sunyi magana da dadewa sannan ya katse wayan dakanshi yamusu booking first flight na gobe da safe sannan yasake kiran sister nashi yace zasu biyo jirgin safe gobe suzo koya ake ciki tadinga gayamai yatashi ya idasa shiryawa duk mood nashi ya chanza sannan yafito anan falo yaga Aman da Amal suna kallon cartoon a iPad nasu duk an musu wanka sunyi kyau gwanin ban sha’awa kaman ya debesu yafita dasu Amal kaman ba itane mara lafiya ba karasawa yayi inda suke ya duka yamusu peck agoshi yace “Dady zaitafi aiki” dasauri Aman yace “Dady zan bika office” shiru yayi kaman mai tunani yana shafa kansu yace “shikenan zanje daku amman sai ranan Saturday jibi kaga gobe akwai school yau bakuje ba dukanku” Dasauri Aman yace “hadda Anty Ummi zamu itama taje taga Daddy’s bigggggg office” ya ware hannunshi biyu yana nuna how big office na babban shi is, dan murmushi yayi yana kallon Aman din kafin ahankali yace “yes Son hadda Anty Ummi” dasauri Aman yace “love you Dady u the best Dad ko Amali? Dadyn mu is the best” dasauri Amal yace “yeeeessssss Dady is the best” murmushi yayi yace “my princess and my Aman are the best nima” harzai tashi yace “ina take?” Aman yace “Anty Ummi”? Gyadamai kai yayi dasauri yace “itama taje tai wanka adakinta” jinjina kai yayi yamike yace “to natafi bye” bye sukamai yawuce yafice. Wani babban shago ne girmanshi zaiyi wani super market din sama da kasa ne, kasan abayoyi ne irin na yan millions din nan designers dan babu abayan yan 100 ashagon saikuma sama asalin designers bags da shoes ne latest collection ma kuwa, zaune take cikin wani office dake nan sama babban office ne na gaske dawasu mata guda biyu suna hira, daya daga cikin matan biyu ne tadaura tissue kan idanunta tana kuka Hadiza taje tsaki tace “kodai nazo nai magana da mijin nan naki ne Baraka”? Dasauri Baraka tazare tissue dagakan idanunta takalli Hadiza idanunta sunyi jazur tace “so kike ya koreni? Not everyone is as lucky as u are kinada miji kaman Nura mai hakuri da share magana, idan nama Ubale abinda kikema Nura saiya lakadamin duka halan saiya korani gida” wacce ke kusa da itane ta tureta tace “dallachan ai gashinan saisa sai gallaza miki azaba yake waya cemiki anama maza good girl yanzu??” Dasauri Hadiza tace “ahh tohh tell her ooo my dear, tell her Zee cus good girl no dey pay again, kima miji good girl ya tattakaki yayi using naki do dambu yaje ya watsar a shadda, ai yanzu zaman Auren fire for fire ake yana baki kada kibari yakai kasa give him back gbasgbos kawai saikaga yasha jinin jikinshi yasan keba kanwar lasa bace, kinga Nura ko giyan wake yasha yasan bai isa ya tunkareni da nonsense nashi ba cus bana ma dauka ne kuma gashinan nasama ma kaina lafiya I do duk abinda naga dama duk abinda raina yaso agidana to waima tsaya idan nai aure banyi whatever naga dama agidana ba yo menene fa’idan auren? Menene banbancin gidan mijina da gidan iyayena? Abeg ke waye Ubale yana cemiki kule kicemai chass wlh zakiga kun zauna lafiya” dasauri Zee tace “Allah yasa ta dauka, itane kullum yamata ihu kaman ubanta, fita saiyaga dama yake barinta, yahanata business ya kulleta agida kullum ciki yake duramata won’t you speak up kinuna mishi kefa duk lokacin dakikaga dama fita zakiyi ki kwatarma kanki yancinki, ki nunamai kedashi are equal sabida yana namiji baya nufin zai dinga juyaki, munafa zamanin feminism ke duk inda namiji yau yataka aduniya kema zaki iya takawa to akanme zaki maida kanki slave dinsa? Jibemu kawayenki yanda muke more rayuwa muncigaba ke kinachan kina bautama mijin dake hanaki fita sana’a, yakuma miki ihu” tissue takara dauka dan maganganun su nasata jin badadi datasan hakane da da Zee tazo daukanta batabita ba, tace “nidai kubarni duk randa nazo wajenku saikun sani ina feeling bad inajin kaina kaman banda sa’a aduniya, kaman I’m the unlucky one, Ubale na sona ina sonshi kuma ya isa yace nayi nayi karnayi karnayi ya is…….” Mtswwwww Hadiza taja tsaki dayasa Baraka tai shiru takalleta Hadiza tace “takuraki dai baya bari kiyi yanda kikaga dama, imagine yaranki uku har yanzu kece ke komi agidanki, girki, kula da yara uku fa da sauransu ke jakace Baraka? In nice ai sai na mutu, Idan yana sonki bazai sama miki yar aiki ba haba akan mene zaki dinga shiga kitchen kina girki awan nan zamanin da masu kudi ke hiring intercontinental chef yana musu girki agida that’s my next plan ma ni nadauko professional Chef daman na share zancen ne bayan na sami wannan current yar aikin nawa Ummi but still zan dauko” dan murmushi Baraka tayi tace “Allah baki sa’a, kowa nada abinda works for him, ninaji naga kuma zan iyane ne, mubar maganan please kona tashi nayi tafiya ta gida daman Zee takawoni, I don’t have to be like you ladies, tundadai ba dukana ko wahalar dani mijina keyiba ko neman mata Alhamdulillah” dasauri Hadiza tace “to abar maganan amman wlh sabida kawai ke kawarmuce duk tare muka taso da tuni mun rabu dake danni banga dalilin dazaisa kene ke duka aikin gidanki ba mijinki na miki ihu kaman wata jak…….” Karan da wayanta yayi yasa takasa karasa maganan takalli screen din ganin Nuri yasa tai murmushi sosai tajuyo da wayan tace “kun gani” tanuna musu screen din wayanta tace “tsakanina dashi kar tasan kar ne amman jibi yanda yake bibiyana maza fa saida hash treatment kana musu taurinkai ki nuna musu ke fire for fire ce cus sun iya raina mace kai mai sanyi irinsu Baraka” Zee tace “kwarai kuwa Aminiyata”. Tashi Zee tayi takalli Barakan tace “muje mu duba abayoyin to” tashi tayi tabita suka fice ba walwala kan fuskanta, Hadiza na kallon kiran sai murmushi take dake kara fito da kyawun fuskanta saida wayan yayi gab da katsewa ta dauka takai kunne ayangance tace “ka gama nunamin matsayina menene kake kirana kuma yanzu”? Dan shiru Nura yayi yana jinta ba sallama bakomi kafin yamace wani abu tai magana, yana addu’a duk wani namiji dabai Riga yayi aure ba to Allah yarabashi da auren mai baki kaman na Hadiza, saikuma chan yace “Hajiya tafadi abayi yau an kaita asibiti but hankalina bai kwanta ba namusu booking flight na safe gobe zasu taho nan da ita da Amina zan kaita hospital taga kwararren Dr, specialist” wani abu Hadiza taji ya tsaya mata arai zai cigaba da magana ta tareshi tace “wai Nuri what gives you the right kadinga making decision regarding our family on your own eh? Wai meke damunka ne zakace Hajiya bama ita kadaiba harda kanwanka suzo gidana bazaka fadamin ba kaji me zance kafin nan kai kadaine agidan? Kodon kaga gidanka ne? Koma da gidanka ne ai nima ba zaman banza nake agidan ba aure ne yabani gidan dan haka u have no right to invite koma waye into my home without telling me, without seeking my approval” tunda Nura yake baitabajin urge na yadaga hannu ya mari mace ba sai yau wlh he feels kaman yadaga hannu ya kifama Hadiza marin da saiya maida fuskanta keya, keyanta yadawo fuska, mahaifiyarshi ba lafiya bama ta tambaya yaya jikinta ba or anything sai maganan gida, menene agidan? What is house? Me Hajiya zatayi agidan? Yau shekaransu nawa da aure Hajiya bata taba zuwa Abuja bama ballema gidanshi so menene abinda matan nan ke fadi? What can a sick old woman zata possibly iya miki agida tana fama da kanta fisabilillahi?Yanada mahaifiya mara lafiya da zatazo garin abuja for the first time yaje yakama mata hotel ne sabida matanshi batason wani yazo wajensu??? Daurewa yayi yarike zuciyanshi yana controlling anger yadan sauke ijiyan zuciya Hadiza tabugamai ihu da tsawa tawaya. “Ina maka magana kamin banza are you deaf ne or what Nuri? What gave you the right to invite a third party to my house baka fara sanar dani ba” shi Hadiza ke kira deaf??? Innalillahi, cikin wani irin murya datai sanyi sosai tsabagen bacin rai yace “mahaifiyata ce third party Hadiza? Maman mijin dakike aure uban yaranki, kakan yaranmu itane 3rd party”? “Well u can translate it duk yanda kaga dama is none of my business just listen to wat am about to say” tadan gyaran murya tace “first of all bada yawuni aka kawota ba don’t expect anything from me babu abinda ya shafeni da dawainiyan ku, sabida Hajiya bazan fasa fita aiki na ba, kuma bazan shiga kitchen ba, kuma bani acikin tafiyan zuwa asibiti ko rakiya kai infact banda any business with anything dazai faru daga goben nan zuwa harta bar gidan, dan haka kaika sani ni please sai anjima I am busy with work, I don’t have time for ur unnecessary demand” ta katse wayan Nura yadade yana kallon wayan kafin ya fuzar da iska kaganshi dole kai saluting nashi dan namiji ne mai hakuri dayay composing kanshi bai duramata zagi ba, dama kiranta yayi yaroketa kada taje aiki gobe sabida su Hajiya sannan kuma ya tambayeta me da me babu agida amman jibi abinda tayi rasa abinda zaiyi yasa yayi dialing number Gardner na gidanshi ruwa ringing daya ya dauka anatse Nura yace “Amadu banda number Ummi danje ka buga kofa ka bata wayan” dasauri Amadun yace “gasuchan inajin muryansu a garden takai yaran suna buga kwallo bari nakai mata” anatse Nura yace “ok”. Bata wayan Amadu yayi yace “gashi Alhaji yakira zai magana dake” sa wayan tayi a kunne kaman yana gabanta ta duka tace “Alhaji ina wuni” baisan what just happen ba amman har cikin zuciyanshi yaji sanyi aranshi na muryanta, dan ijiyan zuciya yasauke ahankali yace “Ummi mahaifiyata da kanwata zasuzo gobe dasafe Mamana bata da lafiya zataga likita agarin nan” da zuciya daya Ummi tace “Subhanallahi Allah yakara sauki, Allah yasa kaffara ne, Allah kuma ya iso dasu lafiya ya tsare hanya” Wallahi he cannot even explain wani kalan dadin addu’an ta da sanyinsu dayaji aranshi, jin yanda yayi shiru yasa Ummi tace “Alhaji kanaso na gyara musu wajen kwanan su ne namata abincin da marasa lafiya keson ci”? Harga Allah ta dauka abinda takira yafada kenan cus ana bata wayan abinda yafara fada mata kenan mahaifiyarshi ba lafiya kuma gobe zatazo. Yarinyar nan is not just good with kids tanada great sense of humor tanada hankali tasan meyakamata and tanada natsuwa, though abinda yakira was yanaso ya tambaya menene babu agida but tambayanta made hum wanna talk to her more, ahankali yace “menene abincin marasa lafiya Ummi”? Kai tsaye dan babu komi aranta tace “meke damun Mama Alhaji”? Yanda tafadi Mama ba Hajiya ba dan yasan batasan Hajiya ake kiranta ba wani sanyi yaji aranshi baisan lokacin dakaman wani dan karamin yaro yace “ciwon sugar da hawan jini ke damunta” dan shiru Ummi tayi kafin ahankali tace “abincin dayakamata tanaci abinci ne da babu sugar aciki, babu Gishiri kuma dan Gishiri yana kara hawan jini, zan mata tuwon Alkama ko tuwon garin plantain dabai nunaba amman duka biyun bamu dashi agida, da miyan ganye, Gwaggo na a kauye nada hawan jini da ciwon sugar duk nasan irin abincin datake ci dake taimakamata bata cika ciwo sosai ba, idan Mama tazo itama zan dinga dafa mata zakagani zata ji sauki da izinin Allah” dan murmushi kadan yayi a tsane yace “nagode Ummi kituramin sunan abubuwan da zan sayo dakuma abubuwan da babu agida, saiki gyara musu wajen kwanan” Ahankali tace “to” dan shiru yayi itama tai shiru tana jiran taji ko akwai wani abun jin shiru yayi yawa yasa tace “hello” batare daya amsa ba yace “inaso naci tuwon shinkafa da miyan taushe ki dafamin kinji” yanda yayi maganan ataushashe saida taji wani iri dasauri tace “too” yasake shiru itama tai shiru tana sake jiran maganan shi maganan su Aman da Amal dayaji suna Anty Ummi come come let’s continue yasa yace “to saina dawo ko” ahankali tace “too Allah dawo dakai lafiya” lumshe idanu yayi tareda zare wayan daga kunne he just wish da matanshi yayi dis dogon magana wlh babu abinda yake craving yanzu aduniya irin kwanciyan hankali, Allah ya azurtashi, yakuma bashi yara, kwanciyan hankali ne kawai yarasa, yesterday yafara magana da yarinyar nan why is he enjoying conversation da ita haka?. See y’all Saturday 🥰 Let’s keep HADIZA in one place, one of the major abu dake kawo matsala agidan miji is shigowan baki, guest ko visitors aturence. Mata will always say ban isa nakawo baki batare dana sanar dakai wane ko wance zatazo ba. Maza kuma sai sun gama cema mai zuwa Allah kawoshi lafiya za’a cemiki babe wane ko kaza na hanya fa zaizo ko zatazo tamana kwana biyu hakan na batama Mata dayawa rai. My question is, is it okay for mijinki ya yarda kowa yazo kafin yazo yafada miki daga baya wane ko kaza zaizo? Koko yakamata yafara neman yardanki ne kafin wane ko kaza yazo?? Cus I keep wondering gidan aure belongs to waye exactly?? Does it belongs to the wives ne sabida ai cewa ake za’a kaiki gidanki ko it belongs to mijin kadai ne koko gidan aure belongs to the TWO OF YOU??? To idan gidan na dukanku ne biyu maisa ba’a making decision kan wanda zai shigo tare??? Mata ayanzu daku nake ko sabida maza sunsan mun tsani ace wane ko kaza zaizo ne koda an gayamana bazamu yarda ba saisa gwara suyi accepting wane yazo kafin asanar damu cewa wane zaizo rana kaza???? How do you think za’a iya magance yawan issues da ake samu idan za’ayi baki agidan miji?? Let’s discuss this👇🏼 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR Novel din nan is FREE bana kudi bane. Chat me up don saki a group wa.me/+2347012181461 EPISODE 4️⃣ Wuraren 7:30 Hadiza tashigo gidan gabaki daya ranta amugun bace yake, Aman da Amal sai Ummi ne afalo dukansu ukun suna zaune kan dogon kujera suna kallon videos letters sound for Amal dudda Ummi bawani boko tayiba iya kanta JS3 but ta iya all this basic things na school shima sound din dan bata iyabane zamanin su da ABCD sukai karatu ba da sounds ba saisa suke koya tanan youtube yanda Amal ke koya itama haka take koya dan sabida koya musu, jin an bude kofa kai tsaye ba sallama yasa suka jujjuyo dukansu hada idanu Ummi tayi da Hadiza dake mata wani kalan kallo dayasa dasauri tamike tsaye daga kan kujeran ta duka kasa danta gane kallon me take mata cike da girmamawa tace “barka da dawowa Anty, ina yini” Hadiza da dama ta shigo da mugun bacin rai dan tun kiran da Nura yamata ashago ranta yake abace tace “ke ban gayamiki koda wasa kada duwawunki yazauna akan kujerun gidana ba, ke kinada darajan dazaki zauna inda nake zama ne yar aiki dake, ubanwa yagaya miki yan aiki nada matsayin zama akujerun gida” Ummi da kanta ke kasa ahankali tace “kiyakuri Anty mancewa nayi Amal muke koyama karatu” baki Hadiza tabude zatai magana daga Aman da Amal da duk suka tashi suna kallon Maman nasu Aman yace “stop shouting at Anty Ummi Mommy” dasauri takalli yaron ta ballamai harara, turo baki Aman yayi yace “u are always fighting and screaming Mommy our school teacher tace anger causes sickness” hararanshi Hadiza tayi bata tace “nakusan fasa bakin nan naka mara kunya kawai” turo baki yayi dan haushin Mommy shi yakeji sosai sabida yanda koda yaushe fada takema Anty Ummi su, bata sake cewa komiba tun maganan Aman tacire heels din dake kafanta awajen tawuce dinning straight taja kujera ta zauna tana sauke jakanta kan table din tace “idan kinga dama kizo kibani abinci” tashi Ummi tayi da sauri ta taho dinning din Aman kuma yakoma kan kujera yayi zamanshi yadauki IPad itakuma Amal tayi hanyar dinning din cikeda shagwaba tace “Mummy babuuuu, ki goyani zanyi bacci” cikeda masifa Hadiza ta nunata da yatsa tunkafin takarasa dinning din tace “don’t even come here wuce kitafi wajen Aman kiyi karatu yanzun nan nadawo zaku fara damuna, goyon kaniyanki zan miki, jeki jira yar aikinku tazo tagoyaki, Oya go back” juyawa Amal tayi tafashe da kuka dasauri Ummi takalleta kaman tadaina serving Maman taje ta dauketa, ta tsani taga yaran na kuka wlh har cikin ranta, ahankali tawuce wajen Aman tafada jikinshi rungumeta yayi yace “stop crying Amali Anty Ummi is coming yanzun nan kinji” Gyadamata kai tayi yana share mata fuska yace “let’s play game”. Tunda Ummi tafara serving tuwo a plate Hadiza ke kallonta zuciyanta na wani kalan tafarfasa kawo tray gabanta Ummi tayi ta ijiye bata idasa jaye hannunta ba Hadiza ta daga tray gabaki daya ta mike tsaye ta kwarama Ummi akai da tuwon dake a leda da miyan taushen da kwanukan da cokulan duka suka bare akanta wani kalan mahaukacin azababben mugun ihu Ummi ta kwala tafashe da kuka dayasa su Aman suka firgita dukansu suka juyo ganin Anty Ummi ta tsugunna a dinning ga miya tundaga saman dan kwalin kanta har goshinta da idanunta ta kullen gam tana ihu sosai jikinta nawani kalan rawa kaman wace ta zare tsabagen azaban zafin datakeji na miyan dakuma yajin miyan a idanunta yasa suka taho wajen da gudu Aman yace “Anty Ummi” cikeda masifa Hadiza tanunata da hannu tace “kina gidana, kinacin abinci na, nabaki makwanci, nabaki kayan sawa, nabaki sabulun wanka dana wanki, sannan ina biyanki kizo bazakimin biyayya ba, sau nawa ina gayamiki ni bancin tuwo sau nawa nake gayamiki? So kike nayi kiba nai katon ciki? Zanje sama nai wanka ki tabbata kin dafamin wani abun kin kawomin dakina kafin nagama wanka inba hakaba wlh saina koraki daga gidan nan this night” ta dauki jakanta tawuce sama fuuuuu, tsugunnawa daga Aman har Amal sukayi agaban Ummi da jikinta har bari yake sabida zafin miyan dan bata dade da gama miyanba ta juye a kulan gidan ga kulan su irin na millions din nan ne masu rike zafi kaman me, dudda Aman yaro ne amman saida yakai hannunshi yacire tuwon daga jikinta yana kuka sosai ya yar akasa yace “Anty Ummi sorry stop crying” Amal tace “Mommy is badddd mommy” sosai Ummi ke kokarin tabude idanunta takasa sai kuka take dudda kukan take na tausayin kanta tariga tai alkawari komenene zatai hakuri tana bukatan albashinta dashi Gwaggo ke zuwa asibiti dakuma shi ake tara kudin auren kanninta, dole ta jure komi itane hanyan cin abincin gidansu, so take ta mike but tama kasa hannunta Aman yakama Amal ma takama dayan yace “let’s go Anty Ummi ki wanke fuskanki” gydamusu kai tayi tana tsayar da kukan datake ta yunkura zata tashi tama kasa saita kara fashewa da kuka daidai lokacin an bude kofa da sauri su Aman suka juyo ganin Baban su shima ya shigo ya tsaya chak yana kallon daga yaranshi har Ummi dake kuka sosai kaman anyi mutuwa agidan ga jikin Ummi duk miya, fuskanta ma haka takasa bude idanu yasa yayi wajensu dasauri baima cire takalmi ba yace “Subhanallahi meya faru faduwa kikayi Ummi” Tsayar da kukan tayi dasauri muryanta na rawan sheshekan kuka tace “eh” tana yunkurawa zata tashi dasauri Aman yace “is Mommy Dady, ita ta kwara mata the whole tray na abinci akai Anty Ummi has been crying” warware handky daya ciro Nura yayi daga aljihunshi baiyi wata wata ba yakai kan fuskanta cikeda damuwa ahankali yace “tsaya” batai musu ba tsayawa tayi kwashe miyan kan idanunwanta yayi tass, miyan yayi fasha fasha awajen harda gashin idanunta, sannan ya kwashe na goshinta dana kumata batare daya taba na wuyanta ba dudda baka ce but he could see yanda fatan fuskan yayi ja, ijiye handky yayi dasauri kafin ahankali yakai hannuwanshi duka biyun yakama kafadanta dagashi har ita atare duka sukaji wani iri dasauri tayi kokari fizge kanta strictly yace “stop banson gardama, tashi muje” yanda yayi maganan ba wasa hakan yasa bata kara gardama ba, yana rikeda ita haka yayi kitchen da ita su Aman suka bisu bude kofan kitchen din yayi zuwa nan backyard gaban wani tap dasuke dashi awajen, yabude tap din yajuyo yakalli Aman yace “je bayin Anty Ummi kadauko mini sabulun wankanta” “okay Dady” Aman ya amsa yajuya da gudu shikuma yabude tap din yace “tsugunna” ahankali Ummi ta tsugunna, gently yadinga tara ruwan da hannunshi yana watsa mata a fuska har saida miyan ya fiffita duka da wayanda sukenan asaman gashin idanunta daidai Aman yakawo sabulan, ga mamakinshi sabulun vivo yagani ahankali ya karbe yakama hannunta yasa sabulun aciki yace “wanke fuskan mugani da sabulu” shafa sabulun tayi ta dirdirje da kanshi yake zuba mata ruwa tana wankewa tass ta wanke fuskan, igiyan wajen ya kalla ganin wata singlet dinshi wanda yasan itane ta wanke yajawo yabata yace “share fuskanki saiki bude idanun nagani” Share fuskan tayi ahankali sannan tashiga bude idanun yajin dataji yasa tamaida idanun ahaukace tarufe tafashe da kuka kunsan yanda yaji ke birkita mutum tace “wlh da kwai yaji sosai Alhaji, wayyoo Gwaggo na nashiga uku” shi arayuwanshi yanada tausayi, ya tsani aga ana hurting mutane in general balle kuma yaga mace in pains, da sauri yasa hannunshi ya karbi hanky yamikama Aman yace “hold it nagani“ sabulun yadauka daga kasa yasa a hannunshi ya fara wankewa sannan ya murza sabulun a hannunshi ahankali yadan kalli fuskanta yanda ta kankame idanunta gam jikinta har lokacin rawa yake tana dan kuka, dan ijiyan zuciya yasauke sannan yakai hannunshi gently yashafa sabulun a fuskanta kaman yanda ake wankema yaro karami fuska, fuskanta is sooo soft kaman na dan yaro, almost 30sec yayi yana chuda fuskan sannan ya kunna pampoo yashiga wanke mata fuskan tass kafin yakarbi singlet din ya share fuskan da kyau ya tsane dogayen eyelash nata kafin ahankali yana tsugunne agabanta yaciro wayanshi dudda akwai haske wajen bauuu flash na wayanshi ya kunna yabama Amal yace “princess haskamin fuskanta” dasauri Amal ta karba ta haska fuskan Ummi, shima yana kallon fuskanta dake sheki yaji wanki da sabulu yace “bude idon nagani” gently tashiga bude idanun dake rawa sosai na haggu tabude tass na dama ne tabude kadan dan tanajin yaji sai yarfe hannu take ta rude sosai ganin yanda takeyi yasa ahankali yace “tsaya” tsayawa tayi ijiye singlet din yayi kan jikinshi yakai duka hannunshi ahankali yayi cupping fuskanta dasauri Ummi takalleshi tadade rabon dataji namiji dab da ita haka, ahankali babu komi aranshi yakai hannanyenshi ya ware kwayar idannun nata dake mata yaji kafin gently Ya hura iskan bakinshi ciki wani kamshi Ummi taji da sanyi daya ratsa jikinta feeling inama ace zata sami miji dazai dinga kula da ita haka kaman yanda Alhaji keyi yanz, Alhaji nada kirki gashi kyakkyawa fari dashi kaman wani balarabe ga bakin saje, tsayar da hura idanun yayi ganin tabude su rass tana kallonshi kaman yaune rana na farko datake ganinshi shima zuba mata idanu yayi yana kallon kwayar idanunta yanda suke walkiya sabida hasken flash da Amal ke hasko musu, idanun sunyi ja na kukan dataci da yanda tai looking so helpless dakuma yanda take kallonshi hakanan saiyaji kaman yasata ajikinshi ya lallasheta, there’s something about her da kawai he finds interesting baisan menene ba. “Anty Ummi yadena yajin”? Maganan Aman yadawo da dukansu daga duniyan tunani atare dukansu kowa ya janye idanunshi, Nura ya mike tsaye da sauri yawuce ciki batare daya kara kallonta ba itakuma ahankali tamike tsaye tana goge wuyanta, gyadama Aman kai tayi tace “yadena” dasauri sukazo kusa da ita suna kallon fuskan hakan yasa ta tsugunna dukansu taba fuskan nata sukayi cikeda so sukace “sorry Anty Ummi” murmushi tayi sosai cikeda kokarin cheering nasu up tawani daga hannunta sama tace “Anty Ummi jaruma ce kaman Amalili, ko Mudi da Kumurci tsorona suke menene yajin miya dashima bazai tsorata dani ba” haba zokaga yanda sukahau dariya, Aman yace “Anty Ummi yaushe zaki kaimu kauyenku muma muga Mudin nan da Kumurci” hannunta takai kan kumatunta kaman mai tunani kafin tace “wata rana zamuje” ihu sukahau yi suna tsalle Nura daya dade yana kallonsu ta window kitchen murmushi yayi yawuce yadauki mop yafice gyara dunning din yayi da kanshi. Shigowa sukayi a kitchen din fita tayi taje dakinta ta chanzo kaya zuwa wani atampa dogon red yamata kyau sosai. Tana fitowa hada ido sukayi da Nura dake zaune a dinning yanacin tuwo adan kunyace ta sauke kanta kasa tazo wajen ta duka har kasa tace “Nagode Alhaji, kana bukatan wani abune dazan kawo maka”? Sosai yake kallonta red yamata kyau dudda babu wani special abu game da atampan but yamata kyau, jin shiru baice komiba yasa tadago kanta ahankali hada idanu sukayi da sauri yadauke kai itama maida nata kasa tayi dasauri, ahankali yace “bana bukatan komi, thank u” mikewa tayi harta juya tafara tafiya kaman daga sama taji yace “abincin yayi dadi sosai, thank u Ummi” dadan sauri tajuyo ga mamakinta kallonta yake suka sake hada idanu sukayi, faduwa gabanta yayi dasauri tasauke kanta kasa tasake juyawa zata shiga kitchen batare datace komi ba yace “mezakiyi a kitchen”? Ahankali tace “Anty zan daurama wani abinci batacin tuwo” strictly yace “wuce kije ki kwanta kihuta” dudda bataso ba dan batasan mezai biyo bayaba kasa musu tayi tawuce takoma dakinta ta kwanta. Fess yagama cin abinci yakai komi kitchen dakanshi yafito yaje sama fitowa yayi da paracetamol, bottle water yadauka mara sanyi yaba Aman yace “kaima Anty Ummi kace nace tasha” gyadamai kai tayi yawuce da gudu yatafi dakinta Amal na binshi yakoma falo yazauna yana saka news duk yanda yaso yama gane meke faruwa a news din kasawa yayi yawuce sama fuuu, bude kofan dakin Hadizan yayi ranshi abace tana zaune gaban dressing mirror daure da towel tana shafe shafen ta na night routine batare da tajuyo ba tace “ki ijiye abincin kiwuce kifita dakikiya kawai next time try this nonsense kinbar gidana kenan jaka kawai yar kauy…..” “Hadiza!” Nura yakirata da kakkausan murya saida gabanta yafadi dan baitaba kiranta da zafi haka ba juyowa tayi da sauri ta kalleshi ganinshi tsaye a tsakiyar dakin yana kallonta ranshi abace, haderai itama tayi tace “badai kahana yarinyar nan dafamin abinci ba dan idan kayi haka u will see the other side of me Nura” wani kallo yamata yace “inason naga other side of you din today are you crazy? Ke wace kalan senseless mata ce? Kissan kai kike kokarin yi agidana? Are you trying to kill that girl?” Hannu ta dagamai tace “please lower your tone ni matarka ne ba some yan aiki dazaka dinga dagama murya ba Nuri, I’m your wife not slave so keeep muryanka down by now kasan I don’t take that shit, namiji yazo yana wani mini ihu akai saikace ubana kuma ma idan na kasheta sai me? Eh? Ba yar aiki bace, yarinya mara galihu duk irinsu ne irin yaran da akauyen su akekai yara maza almajiranci mata kuma akaisu aikatau kota mutu sai me mezai faru? Almajirai nawa suka mutu wani abu yataba faruwa? Ai yara da iyayensu suka nuna basu da gata mutane ma basa gatanta su so bakaina farau ba dan yar aiki ta mutu agidana ehe” Sosai Nura ke kallon Hadiza shi baimasan tayi nisa haka ba sai yau wato tanada answer for anything, at this point baimaso maganan nasu yayi nisa dan kar zuciya ya debe shi yadauketa da mari hakan yasa cikin kakkausan murya yace “duk randa kika sake trying nonsense din nan wlh saikin bar gidane duk wani abu dake gidan nan fara tundaga kan gateman suna karkashina ne, hakki na ne nakare kowa na tsaresu dan haka don’t ever try hurting mutanen dakemin aiki inba hakaba u will leave this house!” dudda maganan ya mugun mugun sosama Hadiza rai amman daurewa tayi dan bataso yagane tai wani kalan shewa. “Ahayyeeee nanaye ance dama idan baka mutu ba bakagama sanin halin maza ba, Nuri ni kakema gorin zaka kora daga this rat hole dakake kira gida”? Ta nuna dakinta da ko’ina da hannu, tsaki kawai Nura yayi yajuya yafita tabishi da sauri dan idan bata bashi amsan maganan nan ba hankalinta bazai kwanta ba kai zazzabi ma zai iya kamata, tana biye dashi yana tafiya tace “zan iya gina gidan dayafi nakan nan sau dubu a kyau dakuma girma Nura kada kayi kuskuren yimini gorin gida, duka duka yaushe kayi kudin lokacin dana aureka kagama masters akan architecture kanama wani building agency aiki har kazo kabude naka kampanin na harkan filaye da gine ginen estate anan Abuja, who do you think you are dazaka min gorin gida nixaka kora Nuri, au ina maka magana ka maidani mahaukaciya kayi tafiyan ka wlh wlh yanda ka batamin rai dinnan saina huce akan mahaifiyark…….” Chak Nura ya tsayar da tafiyan dayakeyi akan staircase yajuyo ahankali yakalleta itama daidai tana tsayawa dab da shi tana kara rike gaban towel nata da kyau tana kallonshi tace “da ilimina da sana’ata da darajata har ka isa kazo kana gayamin na kara dukan wata yar aiki sainabar maka gidan ka, sabida yar aiki Nuri zakace zaka koreni, what on earth do you take yourself for? Are you God? Sabida kaganni mace kadauka I am weak ne I can’t defend myself? Zakace zaka korini daga gidanka u think bazanyi speaking up ba, Listen Nuri, me and you are two equal people! Baka fini da komi ba, duk inda kasa kafa nima zan iya saka kafan, nasan kimata nasan daraja ta and my worth u cannot downgrade me or downgrade my status and for batamin rai din nan dakayi this night wlh saina batama mamank…….” Azuciye Nura yadaga hannu zaikai mata mari kaman daga sama sukaji Aman yace “Daddy!” Chak Nura ya tsaya da hannunshi batare dayakai marin ba, he don’t ever wants yaranshi to have a memory of him yana dukan mahaifiyar su, dunkule hannunshi yayi tareda saukewa kasa ahankali yajuyo yakalli Aman din, dasauri Aman yazo ya rungumeshi tsamtsam yana kuka sosai yace “Daddy sorry kayakuri Mommy is sooo baddd but don’t slap her okay Dady, beating girls is not good katuna ranan dana daki Amal haka kagayamin” daukan yaron Nura yayi ya rungume ahankali tareda mannamai kiss akai yama kasa magana yashiga tafiya dashi yana sauka, Hadiza dake kallonsu tace “ai naso ka maren wlh danai suining naka for domestic violence, try that next time kagani I will mess you up Nura” sauka yashiga yi kasa yana dauke da Aman a hannunshi gaban dakin Ummi yakaishi yace “shiga” shiga yayi sannan yajuya yawuce yafita daga gidan yashiga motanshi yamabar estate din gabaki daya zuciyanshi daci takemai da gaske idan Allah yabaka mata nagari wlh ka gode kama kara godemai dan shaidanun mata azaba ne, they will so push you to the wall kaji kaman zaka kashesu, yayi tafiya mai nisa sannan yayi parking yakalli wayanshi yadade yana kallo kafin yasauke ijiyan zuciya yakai hannunshi yadauka yabude yaciro wani lomba yakira wayan na gab da katsewa aka dauka daga dayan bangaren wata yar dattijuwan manyantaccen murya ne tai magana. “Nura barka da dare ya wurinku yasu Amalily?” Ahankali yace “lafiya lau” saikuma yayi shiru all this years baitaba daga waya yakai karan matanshi ba sai yau jin yanda baiyi magana ba yasa tace “lafiya Nura Maiya faru? Ina ganin wayan nasan da wani abu duba da lokacin dakama kirani, what happened?” Ahankali yace “Hadiza bansan menene damuwanta ba, tunda na auri Hadiza Anty Jamila for once bantaba kokarin takata ba ko shut her up, ni mutum ne dana tsani takurama mata ko basu damuwa I have 4 sisters dukansu mata nataso da sanin yanda ake girmama mace kare mace dakuma daraja mace” Anty Jamila tace “kwarai Nura wannan haka yake zan shaideka ako’ina” ahankali yace “the whole idea da concept na feminism ya shiga kanta, I’m not saying feminism is wrong no, ko Allah yasani inaso naga matata tacigaba, banki duk matakin dazan taka aduniyan nan matata ta takashi ba, I empower her nabata jari tafara business nakaita su dubai oman Egypt dasauran kasashe alokacin sabida ta saro abayoyi tafara, bansan gobeba I believe empowering matata will go a long way for yaranmu incase of gobe dabata da tabbas, bantaba ma Hadiza kallon wata baiwa ko yar aiki ba rather I see her as life partner dina wacce nakeson to go through every phase na Rayuwa together mu tsufa together but ita bahaka take ganin komi ba, gani take anything daya kamata tayi agida nima yakamata nayi nida ita we are equal, yimin girki gaidani bani abinci is not her duty duka abubuwan nima nayi we are equal afterall, gaidani akan me zata gaidani nima na gaidata…” dasauri Anty Jamila tace “subhanallahi” dan ijiyan zuciya yasauke yace “Anty Jamila the whole feminism din nata haukane kawai, rashin kunya menene menene babu wanda bata mini nakasa gane kanta balle kafanta, i can’t even talk to her kafin nayi magana daya tayi dari, Anty Jamila I am tireddddd nagaji, I want peace of mind at this my age” yanda yayi maganan saida yabama Anty Jamila tausayi tasan yanda Nura keda hakuri tasan for Nura yadauki waya yakirata takaishi bango anatse tace “Nura kayakuri kayakuri shikenan abinda zan iya fadi kaga wannan halin shine dalilin dayasa maza da yawa basason bama matayensu freedom har subarsu suyi sana’a dan wasu matan dazaran sun soma taba kudi shikenan sai sudinga jin kansu kaman giwaye suma yanzu sun faso, amman kabarni da ita zan kirata zan kira Mama kuma” ahankali yace “please kada ki sanarda Mama tana fama da hawan jini saisa nakiraki ban kirata ba” murmushi tayi tace “to shikenan amman dan Allah kayakuri” ahankali yace “to saida safe agaida yara” yakatse wayan yadade ahaka yau bacin ran yasa he wanna be alone ma inda bahaka ba zai iya kiran abokan shi yaji inda suke yaje yasamesu, yayi kusan 3hrs awajen sannan yatada mota yabar wajen. Domin magana dani M shakur koso nasaki a group dina chat me up tanan wa.me/+2347012181461 Yana katse wayan Jamila ta danna mata kira wayan harya katse bata dauka ba akaro nabiyu ne tadauka tace “Hellooo Anty Jamila” cikin fushi Jamila tace “ke wace irin mahaukaciya ce Hadiza? Ni wlh I don’t even need to ask you nasan kene da laifi dan nasan kalan hakurin Nura tunda yau dakanshi yadaga waya yakirani nasan kin mai babban laifi” tsaki Hadiza taja dayasa Anty Jamila tasake baki, cikin fushi Hadiza tace “ohhh kiranki yayi yahada mini munafinci? To wlh zaizo gidan nan yasameni ina jiranshi” jin yanda yake magana kaman tana jiran wani saran wasanta yasa Anty Jamila tace “Hadiza are you okay kuwa? What has gotten into your head? Nuran kike magana haka akanshi?” Cikin fushi sosai Hadiza tace “Anty Jams bazaki gane bane, Nuri finds every little way to belittle me, nan Abuja ne fa ba kano ba but kullum so yake ina shiga kitchen namai abinci, a Abuja yan aiki ke girki matan gida relaxing take bayinta namata aiki, inada yar aiki ai nama baki labari wacce nace miki su Aman na sonta, ita ke kula dasu I am busy da shigo gida nawa yake so naraba kaina? Sai nasa yar aiki tamin wani abu yahanata yimin sabida shike biyan kudin shine nacemai yadena daga this month nizan cigaba dabiyanta sabida I should be the one in control of her, ina shago dazu yakirani wai Mamanshi zatazo gobe taga Dr kinji fa Anty Jamila sabida ya rainama kanshi wayau danni bai isa ya rainamin wayau ba, gidan nan belongs to two of us baida right dazai kawo koma uban waye into this house without asking permission dina, what did he take me for eh? Wlh wlh jiransu nake suzo goben dagashi harsu saina kuntata musu bakin cikin da bazasu kara marmarin zuwa gidana ba me akeyi da yan uwan miji banda hauka mtswwww” “Innalillahi wa innailaihi raji’un” Anty Jamila tafadi tana tafi da hannunta cike da mamaki tace “Hadiza giyar kudi ko giyar karatun wannan femi ah’ahhh Feminism ko oho dai ke damunki” Hadiza tace “feminism wai? I know my right I can fight for my right duk inda nake aduniya tunda mata suka gano this feminism sun samu yanci sun samu cigaba, a woman can stand aduk inda namiji ya tsaya aduniyan nan” “dalla rufemin baki sai idea bature yasa kin rasa mijinki tukunna zaki dawo hankalin ki” Anty Jamila tamata ihu tace “wannan ba shine tarbiyan da aka baki agida ba, keda mijinki can never be equal ko awajen Allah domin ko aljannanki na karkashin tafin kafanshi, mata dakika ganmu daga rib guda daya na maza aka hallito mu, kada ki mata, Allah yafadi acikin suratul Nisa’i aya na 34, Arrijalu qawwamuna Alan nisa, bari madai naja miki ayan gabaki daya ٱلرِّجَالُ قَوَّٰمُونَ عَلَى ٱلنِّسَآءِ بِمَا فَضَّلَ ٱللَّهُ بَعْضَهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ وَبِمَآ أَنفَقُوا۟ مِنْ أَمْوَٰلِهِمْ ۚ فَٱلصَّـٰلِحَـٰتُ قَـٰنِتَـٰتٌ حَـٰفِظَـٰتٌۭ لِّلْغَيْبِ بِمَا حَفِظَ ٱللَّهُ ۚ وَٱلَّـٰتِى تَخَافُونَ نُشُوزَهُنَّ فَعِظُوهُنَّ وَٱهْجُرُوهُنَّ فِى ٱلْمَضَاجِعِ وَٱضْرِبُوهُنَّ ۖ فَإِنْ أَطَعْنَكُمْ فَلَا تَبْغُوا۟ عَلَيْهِنَّ سَبِيلًا ۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيًّۭا كَبِيرًۭا ٣٤ Men are the caretakers of women, as men have been provisioned by Allah over women and tasked with supporting them financially. And righteous women are devoutly obedient and, when alone, protective of what Allah has entrusted them with. And if you sense ill-conduct from your women, advise them ˹first˺, ˹if they persist,˺ do not share their beds, ˹but if they still persist,˺ then discipline them ˹gently˺. But if they change their ways, do not be unjust to them. Surely Allah is Most High, All-Great. Allah ne yafadi da kanshi, idan kuma u are talking about rights da yanci ne tun zamanin Annabinmu ya kwatoma mata yancinsu idan wani yaji kina magana haka idan ba’asan Nura ba zaa dauka wani abu bawan Allahn nan yake miki, kin sami miji nagari bawan Allah shiru shiru mara magana kinamai irin abubuwan nan ke kinada baki kice sai da izinin ki mahaifiyarshi zatazo gidan danda tahaifa, matan da komu nan last week saida muka kirata muka mata yajiki wlh maganan ki yasama ina jin kunyan Nura, Hadiza sau nawa da ni da yarana harda Mama muke zuwa gidan ki every now and then duk wani abu dazai shigo damu Abuja gidanki ne masaukinmu we don’t even ask for permission sabida anzama daya, ace yau mahaifiyarshi zatazo for treatment na rashin lafiyanta kina maganganu haka ina imanin ki? Wani kalan tsantsan son kai ne wannan”? Cikin kunkuni Hadiza tace “ai dama side dinshi zaki dauka nasani mutum yana nema ya maidani yar aiki bazakice komiba ace nine zan shiga dakinshi na gyara namai girki bayan inada yar aiki mai yi” Anty Jamila tayi shiru na kusan 5min sannan tace “danace basai na sanar da Mama ba but Hadiza kinyi nisa Mama dole ta shigo zancen nan, yar aiki itane ke gyara dakin mijinki tamai girki? How many minute zai daukeki kima mijinki girki? Bawai nace yar aiki is bad bane ai ko ni inada yar aiki tadan taimaka maka da one or two things but that does not mean zaki barmata ragaman gidanki menene haka Hadiza ke kina ganin wayau ne hakan kin cika yar boko ko? Kin waye kinada kudi kinyi kawaye matan Abuja kema kin dauki sahunsu kirasa wanda zaki mawa sai mutumin da shine yabaki jarin mutumin that made u Hadiza” ihu Hadiza tayi tace “me aciki Anty Jams ai sai nabiyashi kudin daya kashemin nafara business din harda riba indai hakan zaisa yafita harkata yabarni na Sarara nayi yanda naga dama” dasauri Jamila tace “wai kinsan wane kike aure kuwa? Nura fa kampanin shi shike tashe yanzu ko su cosgrove abayansu suke, ga kyau ga aji ga hakuri baki tunanin yazo yahadu da wata kinamai haukan nan yakaro aure abinshi” har cikin ranta Hadiza taji maganan ya soketa dasauri tace “Nuri baida ra’ayin mata biyu tun kafin muyi aure yamin alkawarin ni kadaice matarshi har abada and Nuri baya taba karya alkawari, he’s a man of his words” dan murmushi Anty Jamila tayi tace “to inhar bakison alkawarin nan ya karye take care of mijinki ki sauke pride din nan youu are under him and u will always be, kidaina mai kallon keda shi are equal kina rainashi, keda mijinki can NEVER BE EQAUL, and Bari nagaya miki ki gaggauta gyarawa kafin Nura ya rufe babinki yabude sabon babi,_ saida safe kuma zan sanar da Mama yanda mukayi” ta katse wayan batare data karabi takanta ba shiru Hadiza tayi tana kallon wayan ranta ya mugun sosu da kalman kishiya. Da Yayanta tayi tsaki tayi ta yarda wayan gefenta tace “shiya isa yama mini kishiya, tsorona bazai ma barshi yayi wannan kuskuren ba, banda hakama mata basa gaban Nuri sai business kuma Nuri baida ma yawan sha’awa kaman nine saimuyi watanni bamubi takan shimfidan juna ba ninama fison haka dan ba haihuwa nakeson nakarayi ba inaso nai maintaining this body da shape shi aina zai taba samun kyakkyawan mata fara hausa fulani komi yaji irina” tayi dan murmushi tanajan bargo takoma bacci abinta. MAISA WASU MATAN KE GANI SUDA MAZAJENSU ARE EQUAL???? 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 5️⃣ Ummi kwata kwata takasa runtsawa koyaya ta kulle ido ganin lokacin da Alhaji ke kallonta take, da yanda ya kula da ita dazun dinnan the same way yake handling su Aman that’s yanda yayi handling nata, abun yaki fita daga zuciyanta, the entire scene ya narkan da zuciyanta sosai dan har yanzu kamshin turarenshi takeji yanda yazo dab da ita, she can still feel dadin kamshin iskan bakinshi lokacin daya hura mata, mirginowa tayi daga dan katifan datake kai zuwa kasan tiles, sanyin tiles din yawani kara tsuma zuciyanta ta bude idanunta tana kallon POP sama fuskan Alhaji take gani wlh Alhaji akwai karisma da haiba dawani irin kyau ahankali tace “inama ya aureni” dawani kalan sauri tadaura hannunta saman bakinta kaman irin wacce tafadi taboo din nan, tayi aiki agidaje 4 wannan ne na 5 bata tabajin kaman mijin ko Alhajin gidan datake aiki ya aureta ba sai wannan sabida yanada mugun kirki, gashi da sanyin zuciya, sannan yanada natsuwa, yanada daraja mutane sannan yana son yaranshi sama da komi kawai mata ce baiyi sa’a ba wlh inda itace matanshi ko zaiga gata dan miji irin Alhaji da baida matsala hakan nan wlh kula zatayi dashi sama da yanda yake kula dasu Amal ma kula zatayi dashi kaman wani jariri tana bashi duk abinda yakeso aduniya, ahaka bacci yayi awon gaba da ita da tunanin Alhaji aranta. Wuraren 1 yashigo gidan da kanshi ya kwaso duka kayan daya sayo dazu na cefene yakai kitchen ya ijiye komi sannan yawuce sama dan kwanciya. As usual biyar yafito sanye da jallabiya tunda yabude kofanshi kamshi ya daki hancinshi ahankali yake sauka daga staircase harya karasa sauka kasa wutan ko’ina akasan akashe wutan kitchen ne kawai akunne ga kofan kitchen din abude wajen dinning yaje ya tsaya yana kallon kitchen din Ummi yagani tana girke girke daban daban ga su lunch bag na Aman da Amali akan island yau zasu school, tana sanye da Riga da skirt yana ganin kayan yagane su kayan Hadiza ne tun tana yammata sun kode sosai amman dudda haka sunma Ummi kyau that means tayi wanka kafin tashigo kitchen folding hannunshi yayi yana kallonta tundaga kan slippers green dake kafanta zuwa kanta dake daure da dan kwalin atampan jikinta, tanada tsayi sannan tanada hips dudda ba sosai ba but sunada curve irin yaran nan ne da suna samin kula zasu cicciko yanzu wahala ne yasa suke looking haka ma, dan lumshe idanu yayi yabude ya tsare fuskanta da kallo ahankali Yatambayi kanshi am I falling for this girl? Dan ijiyan zuciya yasauke yajuya yawuce yafice zuwa mosque yana deep tunani shiba yaro bane yasan when zuciyanshi keson abu. Wuraren 7 nasafe yashigo gidan Hadiza yagani a dinning taci gayu sosai cikin wani exclusive atampa ta buga dauri tanacin lafiyayyen breakfast chips da pepper soup sai shayi agefe, itakuma Ummi na tsugunne a tsakiyan falo tana feeding Amal a baki Aman na kusa da su daduk ta shiryasu cikin kayan makaranta suna ganin babansu da gudu sukai wajenshi. “Daddyyy Assalamu Alaykum Dady ina kwana” murmushi yayi yadauki kowannensu yamusu peck yashigo dasu falon yace “ku karasa breakfast yanzun nan school bus zaizo” basuyi musu ba suka koma, anatse Ummi da kanta ke kasa tace “ina kwana Alhaji” batare daya kalleta ba yace “fine” sannan yadau remote yana chanza tasha 8 zai fita hakan yasa kawai ya ijiye remote din yawuce sama ko kallon HADIZA baiyiba itama bata kalleshi ba saima karasa cin abincinta datayi tawuce tadauki car key tace “ki dafamin couscous da daddare ke” ahankali Ummi tace “to Anty, saikin dawo Allah bada sa’a” yatsine fuska tayi bata amsaba tawuce tafita tashiga motanta tabar gidan, bata dade da fita ba motan su Amali yazo Ummi takaisu suma suka wuce tafito tana gyara wajen taje dinning ne ta gyara inda Hadiza taci abinci sannan tawuce tana duba girkin datake ma Kakan su Amal dazata zo, tana cikin tuka tuwon Alkaman taji kamshin turare dasauri ta juyo hada ido tayi da Nura daya shigo kitchen din yasa wani blue gizna shadda wlh yayi kyau na bugawa a jarida faduwa gabanta yayi dasauri ta dauke kai ta saki muciyan a tukunya zata duka yace “cigaba da abinda kikeyi” batai musu ba tacigaba saikuma tadan juyo hada idanu suka sakeyi ahankali bakinta nadan rawa tace “kana bukatan wani abu ne Alhaji”? Dan girgiza kai yayi yaja daya daga cikin kujerun dake gaban island din yazauna yace “me kike tukawa”? Atsanake tajuya takalli tukunyan tace “tuwon Alkama, kace Hajiya da safe zata iso saisa nake mata nasan basuyi kari ba suka shiga hanya, itakuma sister ka zan dafa mata abu daban” yana kallonta yace “nikuma fa” dan kallonshi tayi ga mamakinta murmushi yasakan mata dasauri tace “breakfast dinka nakan dinning amman idan kanason wani abu daban ne zaka iya fadamin namaka yanzun nan” “hmmm!” Yasauke ijiyan zuciyan dashi kanshi baisan karanta yafito ba maganan yatabamai zuciya dan wannan ne abinda matanshi bata tabamai ba just look at yanda yarinyar nan tabashi girma da daraja da kima kome yakeso yafadi zatamai that king treatment shitake mai, kawai saiya dago yakalleta yace “dafamin shayi mai kayan kamshi” dasauri tace “to” zare muciyan tayi daga tuwon tadan diga ruwa ta rufe tarage heat din tawuce ta wanke hannunta tashiga hadamai shayi shikuma yaciro wayanshi yana tabawa dan kawai tasaki jiki amman wlh kusan kome takeyi idanunshi binta suke, nan da nan tahada shayin tadauko wani hadadden flask jug tazubamai tasaka a tray tadauki cup da spoon da sugar kaga yanda take plating zaka dauka taje culinary school ne nan ko tsabagren experience ne a aikatau, tadauko tray din tazo har gabanshi ta ijiye sannan ta duka tace “nazuba maka?” Ahankali yace “yes” mikewa tayi yana kallon hannunta farcenta farare kal dogaye masu kyau tazubamai tace “sugar cubes nawa zansa ko asa zuma?” Kaman wani yaro dan he’s just enjoying the way take neman permission nashi for komi this is luxury da baya samu yace “zuma” dasauri tajuya tafita daga kitchen din taje dinning tadauko zuma takawo ta zubamai sannan tajuya tadauki cup din tadaura kan tray nashi tajuyo tabashi kallon fuskanta yayi sannan yasa hannu ya amsa yace “thank you Ummi” wucewa tayi takoma wajen tuwon tashiga kwashewa kaman daga sama taji yace “waye Mudin kauye?” Juyowa dasauri tayi takalleshi hada ido sukayi yana kurban tea juyawa tayi tacigaba da kwashe tuwon tana mamaki a ina yatabajin takira sunan Mudi saikuma ta sauke ijiyan zuciya tace “tsohon miji na ne” dasauri Nura yakalleta yace “kin taba aure”? Gyadamai kai tayi tace “eh amman an dade tun ina shekara sha uku-sha hudu aduniya” yana kallonta yace “meya rabaku”? Tsayar da kwashe tuwon datakeyi tayi saikuma ta kalleshi yanda ya tsareta da ido yasa ahankali tace “dukana yake, kullum kullum duka, hakanan kaman idan bai dakeni ba bayajin dadi rayuwanshi, shine…..” takasa maganan tai shiru takai hannu ta goge hawayen dasuka zubo mata dasauri tajuya tacigaba da kwashe tuwo Nura yace “shine meya faru”? Ahankali tana kwashe tuwon tace “shine rannan dayamin wani bakin duka saida na haifo bakwaini, inada cikin wata shidda lokacin, amace yafito yaron, saida nayi jinya na kusan shekara daya inata fama da yoyon fitsari, Gwaggo na ta hadashi da mai anguwa akan saiya sakeni kuma abimini hakkina dan ya illata mata jika tun bayan haihuwan dole dayasa nayi ban warkeba, to da kyar yasakeni amman dudda ina rashin lafiyan yakan biyoni har gidanmu yamin duka har suma inayi, ko baizoba kullum cikin fargaba nake zaizo, Maman mu tarasu Gwaggo mu ce kadai garemu kuma batada karfi ta tsufa, ahaka dai na warke but ina cikin tsoro kullum, saisa dataji wata mata dake zuwa kauyenmu kwasan yara aiki taje ta roka da kyar akace za’a daukeni, to aboye aka fitar dani daga kauyen mu kada Mudi yaganni, tundaga nan nazo birni tun ban gane abubuwa harna gane yanzu nima, amman inaso nakoma kauyenmu naga Gwaggo na da kannina Salamatu tai aure harta haihu Maimuna da Ikilima ne za’ayi bikinsu kwanan nan kuma inaso naje amman Gwaggo na bataso nazo tsoro take kada nakoma kauye Mudi ya kasheni, yanzu ance yafi da zama takadiri ya gagari kowa, tsoron shi ake har mai gari, amman nayi kewan garinmu da gidan mu da Gwaggo na da kannina sosai bansan ya Allah zaiyi dani ba bansan kozan kara sa kafa a kauyenmu ba” tai maganan tana kai hannunta saman fuskanta duka biyun tadanyi sheshekan kuka mara sauti, shiru Nura yayi yana kallonta tabashi tausayi sosai ahankali yace “kinaso nakaiki kauyenku kiga yan uwanki”? Dasauri tazare hannayen ta dagakan fuskanta takalleshi da rinannun idanunta yanda ya tsareta da idanu yasa gently ta gyadamai kai, murmushi yayi yace “I promise zan kaiki kauyen ku, and namiki alkawari ba Mudi ba ko mudari yake bai isa yamiki kallon banza bama balle ya dakeki kinji” gyadamai kai tayi ahankali, murmushi yadan mata yace “kada ki kara kuka bayama fuskanki kyau” akunyace tai murmushi shima murmushi yayi yace “idan Hajiya tazo dazaran nagama kata katan asibitin ta zan kaiki gida ko” gyadamai kai tayi dasauri, tashi yayi yakalli agogon hannunshi yace “bari natafi daukosu nasan jirginsu yatashi yanzu kafin nakai airport sun sauka, kinason nasayo miki wani abu”? Yamata tambayan da saida ta kalleshi da mamaki ganin ya tsaya yakuma tsareta da ido tace “Amali tadameni tun jiya zatasha yoghurt babu yoghurt agida” jinjina kai yayi irin yaji din nan yace “ke me kikeso”? Sunnar da kanta kasa tayi akunyace tace “slippers wannan yakatse dazu na naneshi da wuka mai zafi saisa na iya sawa” yanda takejin kunyanshi na burgeshi sosai, anatse yace “to” yajuya zai wuce dasauri tace “Nagode Alhaji Allah kara girma, saika dawo Allah ya tsare” juyowa yayi yace “Ameen Hajiya Ummi” dasauri takalleshi wucewa yayi yafice yana murmushi mota yashiga, saida yafara tsayawa a super market yayi sayayya harda cream da shower cream mai kyau yasa mata da su turaruka da wasu abaya daya gani a super market din da idanu ya gwada tsayinta haka yabiya kudi yafito, haryakai airport labarin Ummi yake tunani yaushe kauye zasu dainama yara Auren wuri ne haka, yanzu sabida wani katon mugu aka koro yarinyar nan aiki, yayi traumatizing nata tun tana 14, small girl fa, hmmm Allah ya kyauta. Daidai yana parking awajen parking wayan Amina nashigowa fitowa yayi daga motan yana daukan wayan yace “okay ku jirani a arrival din gani nan zuwa” wucewa yayi tun kafin su ganshi ya hangosu, wata tsohuwa ce fara mai zanen kalangu a fuskanta zaune kan wheelchair dawata budurwa da akalla zatai tsaran Ummi ke gungurawa ga akwatinan su kan cart a gefe tareda mutumin dake turawa, ahankali tsohuwan matan tadago idanunta dan taji alamun danta ajikinta hakan yasa sai waige waige take, ta baya yazo yahada idanu da Amina daya mata alamun kartai magana sannan yataho kawai Hajiya ganinshi tayi agabanta ya tsaya bai damu da airport sukeba tsugunnawa yayi yasa guiwowinshi akasa yana kallon fuskan mahaifiyar tashi data washe baki ganinshi tace “me haka tashi tashi kayanka zasu baci, yanzu kasan banda karfi balle na wanke maka” ahankali yakai duka hannayenshi yatallabo fuskan mahaifiyan nashi yace “bance kada ki kara ciwo ba eh Hajiya?” Cikin barkwanci tace “ai dazai tasomin saida nace kai rashin lafiya ka manta kashedin da Nura yamaka ne kakeso kadawo kuma” dan murmushi yayi duk rashin lafiyan Hajiya bakinta is always there baya fatan tai rashin lafiyan dazai hanata magana har abada In sha Allah. Rungumeta yayi ahankali yace “barka da zuwa Mamana, Allah yabaki lafiya Hajiya, Allah yasa kaffara ne” bayanshi ta shafa tace “Ameen Ameen ai naji sauke Amina ai bata kyautamini ba banso ta tadamaka da hankali ba wlh, tashi daga kasa kaga jama’a sai kallemini d’a suke yasa guiwa akasa” batare daya saketa ba yace “albarkan mahaifiyata nake so” murmushi tayi tace “Allah maka albarka Nura, Allah ya lura dakai kaman yanda kake lurada ni, Allah yasa yaranka sumaka yanda kamini Nura, yanzu tashi mutafi kaji dan albarka” anatse yace “to Hajiya” sannan yadago yabama mai cart hannu suka gaisa sannan yakalli Amina hannu yabude mata dasauri ta rungumeshi tace “Yaya ina yini” kanta yashafa yace “lafiya lau Autan Hajiya” wheelchair ya karbe yashiga tura Hajiya da kanshi har mota saida ya zaunar da Hajiya tazama comfortable sannan ya sallami mai cart suka shiga mota suka tafi, Hajiya sai kallonshi take ta madubi tanamai hira tace “amman kai rashin lafiya ne ko Nura? Naga kafada sosai”? Dan murmushi yayi yace “aiki ne wlh Hajiya” ijiyan zuciya tasauke tace “to Allah yabaku sa’a kadinga hutawa kanacin abinci akai akai kaji ko” “to Mamana” ya amsa yana murmushi, tace “nataho maka da danderu” baki yabude yadan juyo zai kalleta dasauri tace “kul maida hankali tuki kake” dan dariya yayi yace “Meenah ya akayi akabar Hajiya tawuce da danderu”? Dan dariya tayi tace “ba anga batada lafiya ba babu wanda yayi musu da ita” murmushi kawai yayi yace “inason Mamana Ameena sosai” Hajiya data washe baki tace “nima inason d’ana sosai” Ameena ta turo baki tace “Hajiya nifa” dan dariya Hajiya tayi tace “Inason ku duka akwai wanda ma yasamu soyayyata irinki Auta na” ahaka suna family hira sukakai gida Nura yace “specialist danai consulting yace zai ganmu by 12 yanzu zakici abinci kihuta anjima saimuje asibitin ko” yayi maganan tareda yin Parking yafito da ita sabida dakali da kafanta tayi tafiya tana rikeda shi suna tafiya ahankali Ameena biye dasu tana kallon hadadden gidan, bude kofa sukayi suka shiga ciki wani lafiyayyen kamshi yamusu sallama dasauri Ummi tafito daga kitchen tazo har tsakiyan falon ta duka tace “sannu da zuwa Mama, ya hanya ya jiki, Allah yabaki lafiya Mama, Allah yasa kaffara ne” washe baki Hajiya tayi tana kallon Ummi tace “waye wannan yarinyar mai ladabi ba irin su Auta ba da basu gaida mutane da kyau, ga iya addu’a, waye ita”? Dan murmushi kadan Nura yayi yace “Ummi sunanta” daidai Hajiya na zama, Hajiya tasauke ijiyan zuciya tace “jiki Alhamdulillah Ummi, sannu kinji Allah miki albarka tashi tashi ki zauna, ina Hadiza? Nasan jikoki na ana makaranta ina Hadiza?” Hajiya takara tambayan da zuciya daya tana waige waige neman Hadiza, cikeda hikima Ummi tace “tadanje tadawo wani uzuri yakamata amman tace na kula dake da kyau kome kikeso namiki” sosai Nura ke kallon Ummi yanda yarinyar keda hikima baitaba sanin zata iya fadan magana hakaba, dariya Hajiya tayi tace “ayyooo” kallon Amina data shigo da jaka Ummi tayi gateman biye da ita da kayansu da sauri ta tashi tace “kawo nakai miki daki jeki zauna kihuta kinsha hanya” murmushi Meena tayi tace “thanks” kai kayan sukayi sama sannan Ummi tadawo tashiga kitchen a tray tajera abincin Hajiya da ruwa a bowl mai kyau na wanke hannu tafito takawo har gaban Hajiya, Hajiya tace “Ayyah sannu da aiki Ummi, Allah dai yasa cimata ne dan yanzu bakomi nakeci ba, cuta batayi ba” tai maganan tana bude kulan ganin tuwon Alkama da miyan zogale dayaji ganye yasa Hajiya tace “laaaaaaa Hadiza tamin girkin nan kafin tafice” dasauri Ummi tabude baki zatace eh Nura yace “Ummi ta dafa miki Hajiya” kara kallon Ummi Hajiya tayi saikuma ta nunawa Meena Ummi tace “kinga girkin sa’onninki ko ke sai shegen kiwuya, wai wannan kamshi haka bari naci abincin nan akasa zan zauna ma” da taimakon Nura tazauna akasa ta wanke hannu takai abincin baki saita kalli Nura takuma kalli Ummi takara kallon Nura again tace “Ummin nan dai danake gani tai girkin nan”? Gyadamata kai Nura yayi sai kawai Hajiya tace “Allahu Akbar wlh tayi girkin yanda nakeso, kaga ba gishiri ba magi, sannan bata sakamin jan nama ba hanta da Koda kadai ne amiyan, cimata tamin kuma yanda nakeso, bani jakana Meena kigani” bata jakanta Meena tayi Nura ya karba, dasauri Hajiya tace “ciro duka kudin dake purse dina” murmushi yayi ba musu yaciro dubu goma da dari biyar ne ta karba tamikama Ummi tace “ga tukuicin ki dan kin dadada mini rai kinsa natuna na diyata Aisha mai bin Nura tana aure a eygpt ita kadai kemini abinci irin wannan taste din wannan tarban da akamin bazan taba mancewa da ita ba, nagode ko Ummi amshi kudinki” akunyace tace “Mama kibar shi ni nadafa miki ne kawai wlh” Hajiya tace “laaaa ungo amshi nace” dan satan kallon Nura tayi shima kallonta yake ahankali yace “bazaki amsa kudin Hajiya ba kinsan kalan makon Hajiya kuwa? Ba kasafai akecin kudinta ba, ke kinyi sa’a tabaki” dariya duka sukayi harda Ameena, Hajiya tace “atoh dan haka karbi abinki” gently Ummi tasa hannu ta amsa ahankali tace “nagode Mama Allah ya ninka miki dubun su” Hajiya tace “Ameeen Ameeen” Ummi na murmushi takalli Ameena tace “nadafa miki shinkafa dafa duka dakuma taliya na manja wanne zan kawo miki” dasauri Ameena tace “taliyan manja” harzata tashi saikuma tadan kalli Nura dake kallonta kasa kasa tace “Alhaji mezan kawo maka bakayi breakfast ba kaima” abincin Hajiya yakalla yace “zanci abincin Hajiya” gyadamai kai tayi tawuce kitchen karaf akan idanun Hajiya yanda Nura ke kallon yarinyar amman batace komi ba, saida sukaci sukai kat Ummi takawo mata juice na cucumber kadai data mata Hajiya tasha sosai sannan Nura yakaita sama dakinsu dakin dake kusada na Hadiza inda Hadiza ta kwana ranan ta gyara Hajiya ma sai complain take ita batason sama Nura yace yafiso ta kwana inda zai dinga jin motsinta hakanan ta hakura. Wuraren 12 suka fice asibiti Ummi tasake gyara gidan. Sai wajajen shidda saura suka suka shigo gidan da gudu daga Aman har Amal sukazo suka rungume kakansu abinci Ummi takawo, tama Hajiya unripe plantain porridge datasa shuwaka da bushashen kifi da daddawa aciki shima ba maggi ba gishiri sai kamshi daddawa da kifi sun bama abincin taste, tayi jellof rice da naman rago ma sauran mutane, duk suka baje harda Nura za’aci abinci anan falo, Ummi takoma gefe ta duka Hajiya tace “kema taho nan kici, an taba haka ki mana girki saiki koma gefe, tahonan” dan satan kallon Nura tayi shi harya faracin faten Hajiya ma, da idanu yamata tazo nan, hakanan taje tashiga cikinsu suka faracin abinci, ita da Ameena da su Aman shinkafa sukeci, tunda tafara aiki yaune rana na farko data ji kaman tana gidansu Hajiya ne Gwaggon ta Amina kuma yan uwanta, sai hayaniya su Amal keyi anacin abinci, no wonder Alhaji keda kirki mahaifiyar shi batada matsala at all. Nura yace “Hajiya dan ban juice din cucumber dinki nasha” jug din Hajiya ta kalla tace “kai Nura na tsammaka na tsammaka harna gaji da sammaka wai kaine mara lafiyan nan ne”? Dariya akayi Ummi itama dan boye dariya ta tayi ganin yanda Hajiya keda barkwanci, takalli Nura tace “inje inmaka kaima Alhaji”? Batare daya kalleta ba yace “a’a kihuta zansha na Hajiya” kofi Hajiya ta dauka ta tsiyaya mai rabi ya karbe ita ta shanye rabin tace “Allah miki albarka Ummi zaki koyama wannan shashashan Autan nawa kafin mu koma” gyadama Hajiya kai tayi, Hajiya tace “Auta dukta cinye ke bakici komiba” dasauri Ummi tace “naci sosai wlh” kashigo falon ji zakayi inama haka farin ciki zai dawwama agidan, Nura yana lura da yanda bini bini Ummi kecin abincin tana duba Amal da Aman, chan kuma saita debo tai feeding Amal da mostly wasa take da abincin at this point bazaiyi karyaba yarinyar ta shiga ranshi sosai barinma dayaji labarinta dazu, yaji ta taba aure har ta haihu dudda pre matured birth tayi amma saiyaji yakara natsuwa da ita, wato saisa takeson yaranshi kuma saisa takeda hankali koba komi tanada experience, baison yayi mu’amala da yara masu danyan kai that knows nothing akan aure koba komi tasan menene aure kuma tayi zaman aure, tayi rainon ciki, sannan tayi nakuda, hakan is perfect for him. Sake lura da yanda yake satan kallonta Hajiya tayi daidai nan aka bude kofa aka shigo dukansu suka dago kai cikeda fara’a Hajiya tace “oyoyo oyoyoo, sannu da dawowa Hadiza” tundaga inda Hadiza ke tsaye tabi kowa na falon da kallo da yanda falon yayi kacha kacha dudda bawai kacha kachan yayi ba kayansu ne jaka da gyaluluwa dasuka zuba akan kujera dan dawowansu kenan Ummi ta taresu da abinci sai abincin da Amal da zuzzubar a falon rice din, daidai nan idanunta yasauka akan Ummi dake cin abinci tareda Amina dakuma yaranta akasa tana kokarin bama Amal abinci abaki hankalinta kwance dan akasa take zaune technically batayi laifi ba yau. “Ke menene aikinki? Jibi yanda gidana yayi kacha kacha zama kikayi kinacin abinci? Kina yar aiki waya gayamiki kinada darajan zama inda mijina yake kici abinci eh”? Yunkurawa Ummi tayi jikinta yayi sanyi zata tashi dasauri Hajiya tace “dakata Ummi” takalli Hadiza dake tsaye awajen da taje tace “ninace taci abinc……” “Hajiya dan Allah kidakata badake nake magana ba” Hadiza tayi maganan rai abace dasauri daga Nura har Ameena suka juyo suka kalleta da mugun mamaki itama Hajiya tayi tsuri tana kallonta dan batasan haka Hadiza tazama tasan ta dai da rashin son aiki ko sunzo babban salla Kano dama ba zama take agidanta ba saidai ta gudu gidansu so bata wani zauna da Hadiza one on one na dogon lokaci ba, ganin abun zai zama wani kala yasa dasauri Ummi ta tashi zata juya strictly Nura yace “dawo ki zauna kicigaba da cin abincin ki” cikeda tsoro Ummi takalli Nura gabanta na faduwa tadan kalli Hadiza dake kallonta rai abace ahankali takoma ta zauna abun ya mugun mugun yima Hadiza ciwo dan yaune rana na farko daya nuna bata isaba agaban yar aikin yawanci ba agaban idanunta suke tsiyansu ba, zuciyanta wani kalan baki yayi takalli Nura tace “muzuba nidakai badai anzo har cikin gidana ana nema ajuyamaka kai ba tun yanzu an fara kulla kisisina da shairi ko da sunan rashin lafiya amman bakin mutum rass yazauna yana zakalkalan abinci to wlh muzuba dani dakai” Ameena jitayi kirjinta na tafarfasa badan Ya Nura na zaune wajen ba da wlh saita durama Hadiza ashar wucewa tayi fuuuu tayi sama kunyan duniya rufe Nura yayi abinda matarshi tama Hajiya jiyayi ma abincin ya isheshi kowama hatta yaran jisukayi abincin ya ishesu Hajiya ta kalli Ameena tace “tashi keda Ummi ku gyara wurin” kunya yasa Nura yamike yama kasa kallon kwayan idanun Hajiya yajuya yace “bari nazo Hajiya” baima jira amsanta ba yafice dasauri Hajiya tabishi da kallo saitaji dan nata yabata tausayi. Kayan daya sayo dazu yasa mai gadi ya kwashe yakaima Ummi sannan yaja mota yabar gidan. Abin yama Hajiya ciwo sosai, ya sosa mata rai, ta haifi yaran dasuka girmi Hadiza, yaranta mata uku biyu sunyi aure saura daya, ita Hadiza zatama rashin kunya haka. Dawowa daga kitchen Meena tayi ganin ba Yayanta awajen tazauna kusada Hajiya tace “Hajiya Hadizan nan yar iska ce kuma wlh wlh ta ijiye iskancin ta a inda tasabayi let her not try that nonsense da ke inba hakaba ni kadai na isheta wlh dan idan nakira su Ya Aisha har gida zasuzo sumata shegen duka ba Egypt ba Ya Aisha zata iya barin ko’ina take aduniya tazo muma duk wacce ta zageki shegen duka……” hannu Hajiya tadaga mata tace “banson maganan nan Auta, Matar yayanki ne” cikin fushi Meena tace “koma waye dama nasha gayamiki halinta tunda kika fara rashin lafiya sau daya bata taba kiranki taji yajikinki ba, yar iska kawai mahaukaciya wacce batasan darajan iyaye ba idanma kinci abinci na kanin ubanta kikaci kona danki, okay saitaga kina shurin mutuwa ne zatasan baki da lafiya dakikiya kawai” Hadiza dataji duka maganganun Meena dan saukowa tayi zataci abinci takoma sama saikuma gobe, takarasa saukowa takalli Ameena dabama ta lurada itaba tace “did u just call me dakikiya Ameena”? Dasauri daga Hajiya har Meena suka juyo suka kalleta Meeena zatai magana Hajiya taja hannunta cikeda hikima irin na manya tace “a’a badake takeba Hadiza wani labari take bani daya faru a kano” kwafa Hadiza tayi tace “gwara dan wlh dasaita bar gidan nan yanzun nan kema kibita” fizge hannunta Meena tayi daga hannun Hajiya tamike tsaye tai wajen Hadizan dan rainin wayon ta yayi yawa ta nunata da hannu tace “an kiraki dakikiya dake nake Hadiza idan baki koreni daga gidan nan ba baki cika yar halas ba” Hajiya datake daga zaune tahau yunkurin tashi tana kwalama Meena kira itama Ummi tafito daga kitchen da gudu tazo wajen yaran ma haka daidai Hadiza na nuna Hajiya tace “kinga dakikiya chan not me” Meena batai wata wata ba ta daurama Hadiza mari abaki jikake tasss!!!! Haba sai jini Hadiza ta kurma ihu tadaura hannunta kan bakinta dataji lema lema tacire hannu taga jini ahaukace tace “ni kika mara”? Ta chakume gaban rigan Meena da karfi, dambe sukahauyi ba kama hannun yaro Hajiya tafashe da kuka sosai Ummi tashiga rabasu amman ina basa rabuwa, dukan juna suke sosai bana wasa ba, Meena ta fizge ribbon din gashin nan taja gashin kaman zata cire mata su daga tushen kwakwalwa, da gudu Ummi tayi waje Mai gadin su takira yazo da kyar aka iya rabasu aiko Meena ta bala’in lallasa Hadiza bakinta sai jini yake ta yayyakusheta a wuya da hannu, dudda itama Meena ta daku a hannun Hadizan amman bata sami any ciwo ba kaman yanda tama Hadiza kowa sai nishi yake, shiga tsakaninsu gateman yayi Ummi tarike Meena tace “dan Allah kuyakuri” cikide zuciya Meena tace “kada kice na yakuri Ummi ba’a haifi wacce zata zagan mini uwa agabana banyi wani abu ba, am I even my mother’s daughter idan agabana za’ahau zagin Mamana nai yi shiru eh? Is she mad? Ba’a bata tarbiya agidan su bane? Idan ba’a bataba ni I will give u, dagayau kowace uwa kika tashi zagi zaki tuna diyar wata ta taba miki duka dakika zagan mata uwa, you are very very very stupid to insult Hajiya kinji, shegiya mai halin matan da iyayensu sukama baki” cikin ihu da kururuwa Hadiza tace “wlh, wlh, wlh yau saina kulleki a police station na rantse da Allah, ni kika daka kin san wacece ni anan Abuja? Number one, the most successful business owner anan Abuja, kinsan award guda nawa ke cikin office dina? BBC waye waye duk anyi hira dani, nizaki zo har gidana ki daka? Wlh wlh u are a small girl yau zan nuna miki your place” tana maganan tayi kofa bayan ta fincike key nata awajen tray na car key ta shiga motanta tafice dasauri Ummi tasaki Meena tayi wajen Hajiya dake kuka shikuma gateman yace “ayi hakuri ayi hakuri” yawuce yafita. Dukawa Ummi tayi takai hannunta tana sharema Hajiya fuska tace “Hajiya kiyakuri” da kyar Hajiya ke iya magana tace “Ummi kiramini Nura gobe goben nan zan koma gida Meena batajin magana nasha gayamata zuciya batakai mutum ko’ina, kowani zagi Hadiza tamini sai mene ita ta zaga basaita bartaba akanme zatai dambe da Matar yayanta eh akan mene daga zuwa na garin nan yau yau din nan? To ko warakata na nan nahakura kiramin Nura idan akwai jirgi yanzun yanzun nan ma komawata zanyi kano” yanda Hajiya ke kuka tana bama Ummi wayanta yasa takira Nura, yana dauka yace “Hajiya” ahankali tace “nice kazo gida Hajiya na nemanka” hakanan jikinshi yabashi wani abu daman baiyi nisa ba duka duka yana ta gaban estate nasu fruits yaje saya yasan yanda Hadiza tadawo saitai rashin mutunci saisa baiyi nisa ba at all dasauri ya katse wayan, ijiye wayan Ummi tayi tadauki Amal dake kuka sosai ta goya Aman ma ta lallasheshi dan duk kuka suke sunga anci uwar Maman su, taje wajen Meena dake wajen dinning zaune akasa yanda Hajiya ke kuka yasa she’s feeling so guilty dan yanzun nan hawan jininta zakaga yatashi, yana isowa gidan ko parking baiyi da kyau ba yafito yashigo gidan Hajiya yagani tana kuka sosai yaranshi suma kuka Ummi sai jijjiga Amal take ga Meena akasan dinning idanunta sunyi jazur kayanta ya chukurkude kaman wani abu yafaru dasauri yayi wajen Hajiya ya duka yace “subhanallahi hajiya menene haka?” Cikin kuka tace “kaga Ameenatu yarinyar chan bazata taba daina jamini bala’i aduniya ba, duba jirgi yanzun nan idan an samu mukoma kano nahakura da asibitin Nura bazan iyaba bazan iya da tashin hankali ba” rungume Hajiya yayi yace “ya isa Hajiya ya isa daina kuka muje ki kwanta gobe da sassafe saiki koma” yay maganan trying to just calm her down, yace “ya isa ko I’m here now, everything is gonna be fine”. Sama yakaita yana zuwa wani allura yamata a hannu da Dr yace adinga mata idan anga hankalinta yatashi nan da nan bacci yadauketa yasauko kasa yazo inda Meena take zaune yace “Meya faru?” Baki tabude zatayi magana saikuma tafashe da kuka cikin kuka tafada mai duka abinda yafaru batai karyaba zaiyi magana daidai an bugo kofa an shigo Ummi ce dawasu yan sanda guda biyu ta nuna Meena tace “officer ga tachan” tashi da sauri Nura yayi yana kallon Hadiza da yan sandan guda biyu wanda ganin Nura yasa basu karasa shigowa falon ba duk suka tsaya anan mini parlor dasauri yakaraso inda suke ya mike musu hannu yace “officer lafiya”? Mutumin yace “Madam dinka ne tashigar da kara kan mother Inlaw ta da sister Inlaw sunzo har gidanta sun mata taron dangi anmata duka, kuma munga shaida bakinta da wuyanta saisa muka biyota muyi arresting sai amusu sulhu a police station” ijiyan zuciya yasauke yajuyo yakalli Ummi dake faman jijjiga Amal tana kuka tarike hannun Aman yace “ku tafi sama keda Meena dakin Hajiya ku rufo kofa” dan yasan Hadiza zata iya kamasu da duka kuma, gyadamai kai tayi tawuce takama Meena duk sukai sama, Hadiza tace “ba sama ba ko lahira kukaje sai anyi arresting naku yau wlh” officers din duk suka kalli Hadiza Nura yace “bismillah ku muje waje” binshi sukai waje Hadiza tabiyosu officer da kanshi yace “ki barmu maza muyi magana mana Madam” tsayawa tayi saikuma ta buga tsaki takoma daki, explaining komi Nura yamusu yama nuna musu some magungunan Hajiya dake motanshi yabasu hakuri kan kada suyi arresting kanwarshi, ganin kamalan shi da natsuwan shi duba kuma da babban mutum ne, a well known businessman anan Abuja kuma ba yaro ba sannan sunga yanda Hadizan keyi itama borkonon kanta ce yasa sukai Na’am dudda haka saida suka amshi 20k a hannunshi kafin su tafi, suna tafiya ya tsaya ya jingina da mota yadan sauke ijiyan zuciya baiso ya yanke decision cikin fushi yakai 5min awajen sannan yakoma ciki afalo yaga Hadiza jikin window tana ganinshi ta taho tana ihu tana tafi tace “u bribe them and send them away sabida kar ayi arresting sister ka da Maman ka ko? To rest assure wlh wlh I will so deal with them, wlh saisun barmin gida, babu wani mahaluki dazai shigo gidana and snatched my peace of mind for me to menene amfanin karatun danayi? Ina zaman zamana wata Maman miji ta dawo gidana da zama is that even fair? Ba manyan asibitoci ne a Kano? Why here why Abuja? Let’s be fair fa Nuri, lokacin da Maman ka ke gidan mijinta mother inlaw dinta tazo ta tare mata agida? Then why me? Kuma ace ban isa nayi complain ba? Still sun shigo ur sister nada taurin zuciyan ta daken ni? Ni Hadiza? Wlh u have to choose one koka tattarasu kaje ka nema musu hotel ko ka maidasu kano, this house belongs to me and you Nuri aure yabani gidan nan, dan haka wlh sai sunbar gidan nan” girgiza mata kai Nura yayi, cikin kakkausan murya yace “wlh saidai ke kibar gidan nan not my mom! ki tattara kayanki kibar gidan nan don’t sleep in my house Hadiza, Na Sake Ki SAKI DAYA!”. The foundation of Marriage is built on trust, respect, biyayya and love which I think Hadiza broke all awajen Nura, now do you all support sakin daya mata? Or do you think he should’ve done something entirely different??? Now the major abu da matan aure fears dayasa basason yan uwan miji suzo is because Men always tends to take side din yan uwansu and neglect side na matan su tambaya na anan shine Nura shima yadauki side din yan uwanshi kenan?? Or kuna tunanin he should’ve done better??? As a woman can you stand kiga an zagi mahaifiyarki data haifeki? Do you support action din Meena or not? Dan two things are involve Hadiza matan yayan tane sannan Hadiza ta girmeta far far and surprisingly Nura bai cema kanwarshi Meena anything ba….hmmmm share your two cents on this😞 Now overall tambayata is kuna tunanin basics na mata akan basason yan uwan miji suzo gidansu uhmmm to some extend sunada gaskiya dan maza always takes side na family su gaskiya ne??? How should a family Man dazai sami kanshi a tsakiyan conflict tsakanin relatives nashi da matanshi address the matter?? See y’all Saturday 💃 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR BONUS💃 EPISODE 6 Dum dum dum!! Hadiza taji kalman sakin ya daki zuciyanta kaman saukan aradu cus ko amafarki, like ko amafarki dai wannan bata taba tunanin Nura zai taba bude baki yace yasake ta ba, duk yanda takeson tai kokarin controlling yanda hannunta ke rawa kasawa tayi wani kalan reflex rawa hannayenta suka fara tama kasa magana sai idanunta data kwalaloo kaman zasu fadi akasa tana kallon Nura daya hade rai kaman wanda baitaba murmushi ba aduniya ya nuna mata kofa yace “get out of my house, out!” Yadaka mata tsawan da saida ta firgita, ganin taki motsi yasa yayi inda take azuciye yasa hannunshi yakama hannunta datake rike da key motanta yawani jata dan ranshi yabaci ainun ta daukoma Mamanshi da kanwarshi Police haba nooo enough! Dasauri Hadiza tashiga cewa. “Nuri, Nuri, Nuri” bude kofa yayi yafito da ita har zuwa wajen motan ta yace “get out of my house” dasauri tace “Nuri ni zaka cewa kasaka are u for real? Wait mafarki nake? Nine zaka saka because of your family now can u see why I was against zuwan family miji cause all they bring into your home is chaos? Nuri ni Hadiza zaka saka? Ni zaka kora from my home”? Wani kallo yamata yace “you are dumb, foolish and you are crazy Hadiza, bakin halinki yasa I don’t have any feelings left for you azuciyana, duk matan da have no regard towards my mother can never have space in my life or home dan haka get out, go and do your feminism awani waje not inda uwata take” yana maganan yawuce ciki ya maida kofa yarufe da key yabarshi ta yanda she can’t come in, Hadiza was completely in a state of shock ita Nuri zai saka, ita Hadiza, wajen kofan tayi tadaga hannu zata buga saikuma tace ai sai su Meena su mata dariya damai gadi, tama zubar da ajinta kenan rokonshi zatayi yabude mata kofa kome? Yasaketa tayi tafiyanta mana, deep down zuciyanta cike yake fal da damuwa sai tambayan kanta take ita Nuri yasaka just now? Ita Hadizan nan saki fa? Saki dai datakeji anama wasu matan itama yau anmata so yanzu she’s a divorcee? Ta tambayi kanta saikuma ta juya tashiga motanta tazauna takai awa daya ahaka dataga dai da gaskene yasaketa ta tada mota ta tafi yanzu inama zataje ta tambayi kanta taje gidan kawarta ne? Ina zata? Parking tayi cikin premises na shagonta tai dialing number yayanta ringing daya ta daga kafin Anty Jamila tai magana Hadiza tace “Anty kinga yasakeni ko”? Shiru Anty Jamila tayi irin shirun son gane abinda tayi, saikuma tace “ai yamiki kyau gashinan jikinki yayi sanyi hankalinki yafara dawowa” cikeda karfin hali da tsiwa tace “jikin wa yayi sanyi? Da ace namai laifi ne sai jikina yayi sanyi? Ni Nuri zai saka sabida yan uwanshi wlh zai gane he’s mistaken idan yana tunanin yasakeni kuma na sakun mai wlh karya yake yacimini mutunci haka yakoreni wl…..” takasa karasa maganan sabida kukan daya taso mata tai shiru Anty Jamila tace “kinason mijinki Hadiza, kina mutuwan son mijinki amman bakin hali da al’adan yahudu da nasara yasa kin zama shaidaniya, shine your eye and accept keda shi are not one amman kin dage ke da shi are one kin dage, kin dage kaman bakar mayya accept cewa ba komi ne arayuwan nan must always go your way ba, idan haukan dakikeyi ko feminism din dakikeyi na solving matsala go and solve this one mana da feminism din look at abinda shegen feminism din yasa kika girba saki and this is just the beginning saikin rasa mijinki sannan zaki gane kene da kanki kika saka kanki a wahala, yanzu bama wannan ba Meya hadaku”? Dudda akule take ahaka tabawa Anty Jamila labarin komi salati Anty Jamila tayi tace “wlh da niyyata muna gama maganan nan nakira Nura nabashi hakuri amman wlh, wlh bazan kiraba saidai Mama takirashi, Hadiza uwarsa kika zaga? Wai aljanu gareki ne koko kin fara having mental disorder ne? Konine bazan tsaya wata tazagi Mama agabana ba sai inda karfina yakare, Meena tamin daidai ke baki girmama nagaba dake ba tayaya nakasa dake zasu girmama ki? Kadan kika gani Allah yab…….” Ihu Hadiza tayi tace “ni dama nasan u will never support me what’s wrong with abinda nakeyi? I am just going with the trend? A home belong to the woman so she should be the one to call the shot, Anty Jamila fisabilillahi da aurena agidana amman bazan fadi ajiba banda say, haka akeyi eh? Nasa yar aiki tamin girki yahanata, yasa yan uwanshi suzo bazai tambayi permission dina ba ita Hajiyan haka aka mata eh? Ta kawai shigo gidana tahanani sakat ana cewa batada lafiya kinga abincin danaga tana zakalkala aciki ne tana zuba surutu? Tanaji aka sakeni aka korani bata fito tasa baki ba that’s shows plan work ne, All I ever yearn for and I ever do was to be incharge of my home, kome zai faru inhar it has to do with gidana nizan fadi ayi ba Nura ba, duk fadan dazanyi dashi akan abinne, idan zaimin haka nima zanmai komi yanada abokai yasan haka akeyi a Abuja har kunya nake kar kawayena suzo suga abinda ke faruwa agidana su bahaka sukeyi agidan su ba” dan ijiyan zuciya Anty Jamila tayi tace “Hadiza baka forcing control da ownership, Nura zai iya bari kina calling shots agidanshi idan yaso amman means dakike bi is not right, tell me one thing dakike yima mijinki tell me?” Cikeda bakin takaici kaman ta make Anty Nafisa ganin taki fahimtan ta tace “Anty Nafisa pls pls understand nan ba kano bane this is FCT for crying out load, city of wealth, a Abuja u don’t have to do anything for mijinki as a wife, a woman is a queen dayakamata tanada ma’aikata which I have, su yakamata suyi komi, in this aspect banyi any laifi ba nagaya miki I’m just going with the trend zamanin damuke kenan, I don’t have to cook, sweep, take care of the kids or anything akwai masuyin aikin abiyasu duk wata Anty Nafisa nan ba kano bane kigane there’s nothing extraordinary anan abinda ke faruwa kenan wlh” hmmm! Anty Nafisa tasauke ijiyan zuciya dan lamarin Hadiza mai girma ne tace “Hadiza kinyi nisa are you saying yanzu kuka koma Italy al’adan Italians zaki dauka kicema mijinki dan Nigeria dole sai yayi? When will u understand mijinki bazamfare ne girman kano, Sana’a ce takawoshi Abuja, Nura is educated but rayuwan bokon nan da wayewa tamasu kudi dakikeso shi baya gabanshi, ace yana aurenki bazaki bashi ruwa dakanki yasha ba menenen ma amfanin ki? Wai kuma ahaka bakimai komi kuma kinaso shi yamiki komi, kome kikace yace Naam ko tunda gaki mamallakiyan Nura sannu Hadiza mai fadi aji, yanzu kina ina?” “Shago na” cikeda isgilanci Anty Jamila tace “maisa bakije gidan kawayen naki ba to”? Ahankali tace “ai abin kunya ne suji abinda yasameni, that means I don’t even have any power or influence agidana inhar mijina zai koreni daga gidana sabida yan uwanshi wlh wlh abin nan yamini ciwo Anty Jamila, you have no idea yanda matan Abuja are powerful agidan su amman ni Nura bazai bari nai enjoying that luxury ba, kuma wlh wlh wlh zai sani” anatse Anty Jamila tace “Hadiza keba yarinya bace you’re 32, ke kinsan abinda kike bai dace ba, uwarmiji uwarkice, ita tahaifo abinda kikeso and nurture him, groom him into the man he’s today, miji ba abin wasa bane dazaki dinga experiment naki akanshi, this is just 1saki Nura yabaki, idan ba u wanna loose him for ever ba ki gyara, all it takes is apology, kije kibama mahaifiyar shi hakuri kibashi hakuri ki gyara the way kike abubuwa agidan ki before it will be too late for u kina jina? Idan zaki dawo kano ne kidawo, zandai gayama Mama nasan zata kirashi amman ni Allah yasan bazan iya kiranshi ba take care Allah kuma ya ganar dake kafin lokaci yakure miki”. Katse wayan tayi tadade zaune amota saida aka tafi magrib sannan tafito ta tafi sama tabude shagon tashiga tamaida tarufe tawuce sama office nata ta shiga kwanciya tayi kan dogon kujeranta tayi shiru tanada kudin kama hotel ta kwana abinta amman takasa, takasa zuwa wajen kawayenta kada amata dariya tagama cika baki, da kyar ta lallaba taje tai salla wasa wasa har 12 nadare takasa bacci sai juye juye take yanzu shikenan Nura yasaketa ya koreta daga gidanta shikenan bata da gata? Itane yau da kwana a shago? Hakanan kawai saitaji tana kewan yaranta koba komi kobadan suzo wajenta ba amman muryansu da hayaniyansu datakeji da Ummi is something sai kawai taji tayi kewansu sosai din nan, lema lema dataji akan fuskanta yasa takai hannunta dasauri ta taba ashe kuka takeyi dasauri ta tashi zaune tace “no feminist don’t cry, with or without Nura I can create my world why am I sad? Dan yace yasakeni, yakoreni daga gidanshi? Why nakejin badadi nakasa bacci 9 nayi bacci jibi lokaci yanzu nakasa why?, Yanzu Nura harya isa yacusamin bakin ciki? Then menene amfanin the belief I stand for? The whole feminism an fito dashi ne dan anunama mata they don’t need men or approval na men to survive on this world, all she need is herself” share fuskanta tayi tass tace “Nura kayi kadan kasamin kunci” ijiyan zuciya tasauke tafara fadama kanta words of affirmation. “I’m Hadiza diyar Tijjani, I’m strong, independent and beautiful dudda tsinanniyar yarinyar nan tamin scars din yakushi yanzu awuyana, I’m smart, unapologetic, resilient and bold, I don’t need a man ko anybody to be happy, Hadiza is enough for kanta, a man can’t downgrade or belittle Hadiza, I’m as tall as the mountain ,as hard as rock, as thick as thicker, no one can break Hadiza saidai ni nai breaking, I’m unbreakable, I’m happy, I’m happy, yesss I am happy!!” Tafadi ma kanta tana murmushi tana dukan kirjinta saikuma wasu munafukan hawaye suka kara fitowa daga gefen idanunta tadaura hannunta akan fuskanta tafashe da kuka sosai tace “na shiga uku why am I sad? Nura ni zaka saka awanan sad mode din? Ni Hadiza zakama saki Nura? Ni kanwarka zatama duka sannan kayi throwing dina out kahadan da saki jibeni a shago zan kwana? Ni Nura?? Wlh saina gwada maka kayi da diyar halas wlh kuwa” wani shegen kunci takeji the state datake ciki ita kanta batasan Nura is this important to her ba sosai take sonshi but bata saniba, she’s extremely sad takasa bacci, kaman ta hadiye zuciya takeji tamutu. Wajajen 3:30AM Hajiya ta tashi daga bacci, Meena tagani agefenta dasu Amal duk suna bacci komi daya faru dazu dawo mata yayi sauka tayi daga gadon da dafa bango tafito dakin Nura taje sallama tayi ahankali ga mamakinta bude kofan yayi yana sanye da jallabiya hannunshi rikeda charbi dasauri yariketa yace “Hajiya kin tashi” shigar da ita dakin yayi yamaida kofa yarufe akan couch na dakin ya zaunar da ita shikuma yazauna agabanta akasa yakama hannunta yarike ahankali yace “Hajiya kiyakuri sabida ni Hadiza tamiki rashin kunya yau” girgixamai kai tayi kafin tazare hannunta daga nashi daya rike ta tallabo fuskanshi cikeda tsantsan soyayya irin na d’a da mahaifi tace “maisa baka taba sanar dani abinda ke faruwa agidanka ba? Nura yaushe Hadiza takoma haka? Kamata wani abu ne”? Duk yanda yaso ya daure kasawa yayi ahankali yadaura fuskanshi sanan cinyan Hajiya murya chan kasa yace “Hajiya nagaji I’m tired, sometimes I feel maisa namayi aure? Da auren nan gwara rashin sa but then nakalli yarana Aman and Amal sainace Alhamdulillah Allah has already blessed me with the most beautiful kids aduniyan nan” yayi shiru yace “Hajiya I don’t have peace of mind idan nabar gidan nan kaman kada nadawo tunanin yarana kesa nadawo, babu one single thing da Hadiza kemin amatsayinta na matana and bantaba mata wani abuba, Hajiya sometime ina zama na gayama kaina indai this is wat comes out of auren educated mace to gwara auren gidahuma jahila dazata maka biyayya and be a wife for you cus Hadiza is a wife for herself not for me, tanada masters in business Administration tanada business kudin sun shiga hannunta, yanzu taga am useless koda ace yau zan rabu da ita tanada future she has money, and money is everything idan kanada kudi baka bukatar komi kuma zata iya kula da kanta, everything data mini I tolerated it dudda she’s 32 but kallon mahaukacin yarinya nake mata Hajiya she insulted you today tayi magana dake kaman ita ta haifeki saisa nace tabarmini gida taje na sake ta saki daya” dasauri Hajiya ta kalleshi dago kanshi yayi idanunshi sunyi jaaa sosai yace “Hajiya kin sanni sama da kowa kinsan inada hakuri kawaici juriya dakuma yafiya yaune rana na farko dazan rokeki Al farma kada kice nadawo da ita please I want a break from this auren mu besides I’ve grown feelings for someone kuma inaso naje garinsu na nemi aurenta” Hajiya na kallon fuskanshi tace “Ummi?” Dasauri yace “tayaya kika sani Hajiya”? Dan murmushi tayi tace “sabida nina haifeka” dan shiru yayi chan yace “Hajiya nakamu da son Ummi sosai, tagayamin ta taba aure tama haihu……” yabama Hajiya labarin yace “Hajiya inason Ummi sabida some odd dalilai” ahankali yace “Hajiya nakamu da son Ummi sabida duk wani abu da Hadiza kedashi ita batada shi” yadan sauke ijiyan zuciya yace “inason ta sabida she’s not educated, sabida batada kudi, sabida she’s not independent, sabida she’s innocent, sabida she’s polite, sabida she respects me, sabida she pay attention to me, sabida tanason yara na, sabida she feed me, sabida tana magana dani calmly her voice is so soothing to my heart, I love her sabida she’s weak, fragile, sabida she’s a soft woman not strong woman, ina sonta sabida matace da idan na aureta nine zan zama ragamar rayuwanta and she will let me be the husband and above all nayi istikhara akanta naji azuciyana na natsu da ita, Hajiya inason na aureta amman saikin bani go ahead” murmushi Hajiya tayi tana kallonshi hannunta takai ta share dan guntun hawayen daya fito daga gefen idanunshi tace “na amince kaje kauyensu ka nemi aurenta amman da sharadin kadawo da Hadiza” dasauri yakalli Hajiya, murmushi tamai tace “Nura no marraige is perfect, kowani aure da crisis din dake ciki har Ummin idan ka aureta you guys will have ur differences and issues but what makes Marraige works and last is the ability to work on your issues understand each other better, forgiveness and moving on without holding grudge, kaga all this fadan yanasa akara fahimtan juna, kuskuren Hadiza shine tunanin datake itada mijinta daidai kuke wanda bahaka bane u are the leader and she’s your subordinate dole ta bika, but I’m sure yanzu she learnt her lesson sabida duk ranan da mace zata kwana awani waje ta dalilin saki ranan bata iya bacci mai kyau ko itace da laifi ko ba itace da laifi ba, saki babban abune, saki is powerful, duk randa aka yishi alarshin Allah na girgiza, duk randa akai saki shaidan na party’s jin dadi, duk inda Hadiza take yanzu tana cikin damuwa sosai, kayakuri kadawo da ita kodan yaranku, kada ka manta Annabi yace akama mace saki daya yakamata tana zaune agidanta ne kacigaba da bata ci da sha har zuwa ka maidata dan haka bring her back karka sabama koyarwan addinin mu” dan ijiyan zuciya yasauke yace “dazu Mamanta takirani tabani hakuri I just told her naji” dasauri tace “yauwa ka kyauta, yaushe zakaje neman auren Ummin? Ka sanar da ita kana sonta?” Girgizama Hajiya kai yayi yace “saina kaita kauyensu zan fada mata inaso sai mun koma Munga Dr gobe naji mai zaice game da ke, kafin nasan ranan dazan kaita” shiru Hajiya tayi ita bataso tacigaba da zama agidan nan ahankali tace “koma me ake ciki gobe daga asibiti ka kaini gidan kanin marigayi mahaifinku daganan suma ai zasu dinga iya kaini asibitin ballama nasan magani zaa bani ace nadawo bayan one week, koma menene inason jibi ka maida Ummi gida ka sanar da yan uwanta banson yanda soyayyanta ya kullu aranka tana zama karkashinka shaidan is real kana jina kaje garinsu jibi ayi magana muji me ake ciki idan da hali zasu baka sai adaura auren achan ma sai kaje tareda kanin Babanka da wasu abokan naka, da Meena kuma Ubangiji Allah yasa albarka ni kaina na yaba da natsuwan yarinyar kuma ta kwanta mini arai. Ba karamin fada mahaifiyar Hadiza tamataba kuma tace tabama Hajiya hakuri da Nura, washe gari ba dudda idanunta a kone suke amman kana ganinta tai zuru zuru sanda Mamanta tagaya mata Nura yace takoma har ijiyan zuciya tasauke aboye baro shagon tayi wajajen 8. Around 9 takai gidansu tana parking motanta Nura na fitowa daga gidan rike da Hajiya da Meena suna hira suna dariya yayi wani irin kyau yana sanye da soft material milk yasa sunglasses a idanunshi, hada ido tayi dasu dasauri ta dauke kai haderai tayi tamau ta taho saida tazo dab dasu tace “sannu ya jiki” bata jira amsan Hajiya ba tawuce ciki tabude kofa ta shiga ta bugo kofan Nura yajuya yakalli kofan Hajiya tace “muje kaga 10 fa likita zai ganmu” wucewa sukayi suka tafi. Tunda Ummi taga Hadiza tadawo ta shiga ta natsu tana gama aikinta ta tafi bayan gida a garden ta zauna akan kujeran lilon su Amal da wayanta a hannu tana buga game, ringing wayanta yayi dasauri ta kalla batasan number ba amman tadauka takai kunnenta ahankali tace “hello” anatse Nura yace “Hajiya Ummi” batasan lokacin datace “laaaaa Alhaji yakuri bansan kai bane, ina yini, Ya Hajiya kunkai asibitin? Wani abu kake bukata nayi?” Duk ta jero mishi tambayan atare, cikin kwantacciyan murya yace “Hajiya natare da Dr, tagama ganinshi kuma zan kaita chan Gwarimpa anan zata cigaba da zama gidan kannin Abba na” “okay” Ummi tafadi but zaka iyajin nuna jin dadin ta a muryanta, ahankali yace “kinada katinki na kasa? National identity card?” Dasauri tace “eh inada shi” shiru yasakeyi yace “kituramin hoton shi ta whatsapp sannan ki shirya kayanki gobe zan maidaki kauyenku Adamawa ko?” Maganan yazomata abazata dasauri tace “eh” saikuma chan asanyaye tace “wani laifi nayi”? Ahankali yace “kin manta alkawarin dana miki zan kaiki kiga Gwaggon ki shine zan cika” murmushi tayi taushi tace “Allah yasaka maka da alkhairi” murmusawa yayi shima yace “kinga kayanki cikin kayan danasa gateman yakawo miki?” Dasauri tace “naga slippers dina na dauka, naga wasu kaya duk sainakai store na ijiye” cikeda so yace “nakine akwai wani black abaya mai stones ahannunshi shinakeso kisaka gobe kinji” gyadamai kai tayi kaman yana gabanta tace “to nagode Alhaji” shiru yayi bai sake cewa komiba tagaji da shirun tace “hello” kaman daga sama yace “zaki aureni Ummi?. Matan Abuja! Matan Abuja!! Matan Abuja!!! Haaaaa, HADIZA has been making countless reference daku, the women of Abuja come close are you all the way Hadiza ke suffanta ku? Ance idan miya yayi yaji??? Ai dole yaji ne zai saka miyan yaji ko?? So kunada dogon explanation you guys need to come clean🤣 But then again all I see in Hadiza is so much soyayya for her man but this stupid mentality nata is leading her astray, why must you be the one to call shots agidan mijinki? To shi mijin is there for what? Name ko fame???? Hello Ladies both married and unmarried are you learning one or two lessons from this novel nawa??? But again kuma let’s not be sentimental, mu kalli Hadiza da kyau, all she ever wanted is power which is normal akwai dominating mata dama, itama tanason kawayenta susan tana juya mijinta but maganan yayanta is valid sabida kunje Italy saikice saikin maida mijinki Italian??? Share your 2cents ladies and gentlemen ❤️ See you asabar💃 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 7️⃣ THIS PAGE IS FOR YOU ZEE, MY NUMBER 1 MOTIVATOR, I LOVE YOU❤️❤️ Saukan tambayanshi Ummi taji kaman daga sama saikuma takai hannunta ta taba kirjinta daya buga, to kodai sabida yanda taketa tunaninshi tun jiya yasa taji kaman yace mata zata aureshi? Ta tambayi kanta, me Alhaji zaiyi da itama in banda shirmen tunainta hakan yasa tace “na’am banji abinda kace ba Alhaji?” Ijiyan zuciya Nura ya sauke wlh yadade baiji murya mai dadi kaman na yarinyar nan ba komi nata sanyaya mai zuciya yake, the feelings he’s developing for her is growing a fastest rate, cikin taushashiyar murya dake kashewa mace zuciya yace “ina sonki da aure Ummi zaki aure ni?” Yanda gaban Ummi ke bugawa saida tacire wayan dasauri daga kunninta takifa shi kan cinyanta tadaura duka hannayen ta biyu kan wayan ta runtse idanunta tana breathing so fast this is unbelievable, yasan tana sonshi ne? Yasan tana tunaninshi ne? Ta tambayi kanta takai almost minti daya sannan tamaida wayan kunneta daidai Nura nacewa bakice komiba, itama wlh bala’in nauyi da kunya takeji tace ta yarda haba saikace jira take, kaman yana magana da little Amal yace “Ummimy” yanda yakira sunanta har cikin jinin jikinta taji itama anarke tace “Na’am” cikeda so da bege Nura yace “ataimaka abawa Alhaji amsa eh Hajiya Ummi na” rufe fuskanta tayi dasauri akuma kunyace, murmushi yadan subuce daga bakinta da yaji karan kadan hakan yasa yayi murmushi yace “Ina jinki” Abala’in kunyace tarufe fuskanta da hannu daya tarike waya da dayan hannun akunnenta tace “idan munje kauyen mu ka tambayi Gwaggo na” murmushi yamata shi babba ne this amsan kadai ya wadatar da curiosity dinshi yace “okay yanzu kije kiyi sallama da matan gidan kice mata zakije kauyenku gobe an kiraki daga gida, kada ki fada mata wani abu bayan haka kinji” gyadamai kai tayi tace “toh” dan ijiyan zuciya yasauke kaman kada yayi sallama da ita yace “tom saina dawo” akunyace still tace “mezan dafa maka”? Cikin kashe murya yace “nabarwa Hajiya Ummi zabi” dasauri ta cire wayan daga kunnenta takashe sai murmushi take, amsanshi melt zuciyanta, wai itadai Alhaji keso ya aura ikon Allah, takai awa daya awajen zancen zuci take ita kadai sannan ta tashi tawuce sama sallama da knocking tayi gaban dakin Hadiza akace shigo bude kofa tayi ta shiga Hadiza na kwance kan gado da babban IPad dinta na apple tana kallon cctv footage na shagonta yanda yau takasa zuwa shagon dan batada karfin zuwa dukawa Ummi tayi tace “sannu da hutawa Anty” kallo daya Hadiza tamata tadauke kai tace “lafiya?” Kan Ummi na kasa tace “Anty tafiya takamani kauyen mu gobe!” Dasauri Hadiza ta yunkuro ta kalleta hakan yasa Ummi tace “Gwaggo na batada lpy tace tanason ta gani maza maza” wani kalan harara Hadiza tamata tama kasa magana to idan ta tafi yaya zatayi da yaran nan gashi kafin su sami wata yar aiki dazasu saba da ita sai an wahala, cikeda asalin rashin son ta tafi tace “inhar kinsa kafa kinbar gidan nan da sunan tafiya to kisani na sallameki daga aikin nan kinajina”? Gyadamata kai Ummi tayi ahankali tace “toh” tsaki Hadiza taja danta dauka she will start begging her tace tafasa tafiyar, rai abace tace “sabida dan rashin lafiya ne yanzu harsai anwani kiraki kinbar aikin ki dake ciyar dasu kinje kauye? yanzu ma tukunna kwana nawa zakiyi idan kinje? Kan Ummi na kasa tace “sati daya ko biyu hala” Hadiza jitayi ranta yabaci datana da wani power da wlh saita hana tafiyan nan cus yaranta zasu shiga wani hali yazatayi dasu yanzu? Ga agency nan kokai requesting yan aiki unless akwai akasa shine zaka samu fast Inba hakaba sai an kawo, tsakin takaici takaraja tace “tashi kifita ki tabbatar dai goben kin shirya yaran nan sun tafi school kafin kibar gidan nan dan da sassafe zanje aiki yanda yau banje ba din nan” “to zanyi Anty, nagode” Ummi tafadi tana mikewa tafice daga dakin tawuce kasa yan karikechan ta tashiga hadawa bayan tagama taje tayi girki, yaran suka dawo ta shirya su bayan sunci abinci takaisu islamiyya dake nan cikin estate nasu itama takasa gayamusu zatai tafiya dan tasan kuka zasuyi sosai amman wlh zatayi kewansu sosai. Wuraren 10 yashigo gidan zama yayi a dinning yaci abinci bura busko Ummi tamai da wani miyan veggies mai dadi abincin dayaci saida yabashi tsoro tass yagama yakalli dakinta yayi murmushi yawuce sama ga mamakinshi Hadiza yagani a falon sama kwance kan dogon kujera daga ita sai wani dan black short mai kaman pant yanada lace abakin wandon very sexy, tasaka half vest milk na silk material mai kyau shima, dan juyowa tayi suka hada ido itada Nuran sannan ta maida kanta kan throw pillow ta kwanta tana kallon tv, ita kanta bama tasan maisa tayi gayun nan tazo nan ta kwanta ba, deep down so kawai take ya kulata, dakin Aman Nura yashiga yadubashi yamai addu’a yafito ko kallon inda take baiyiba yashiga dakin Amal yamata addu’a yafito ta gefen ido Hadiza keta binshi da kallon ganin su Hajiya basu dawo tareda shi ba to ya komar dasu Kano ne? Ko yamaka musu hotel ne?. Dakinshi yashiga bayi yafada direct yayi wanka fitowa yayi daure da towel a waist ga mamakinshi Hadiza yagani kan gadonshi ta kwanta tana kallonshi exactly irin kallon shima yamata yadauke kai yawuce gaban madubi ya shafa mai ya feffesa lafiyayyun turarenshi yaje gaban wardrobe yaciro pajamas nashi yakoma bayi yasaka yafito, ganin ya dumfaro gadon yasa Hadiza tasoma jin dadi aranta agaban gadon ya tsaya yasake kallonta ido cikin ido itama kallonshi take right in the eye amman bazata iya bude baki ta gaidashi kota cemai sannu ba taga shigowanshi gida tun dazu, dauke idanunshi yayi daga kanta, filon dake gefenta yasa hannu yadauka yayi wajen kofa yabude yafita yawuce dakin Aman kan gadon Aman yahau yana kashe wuta ya kwanta abinshi yana sauke ijiyan zuciya. Bugo kofan Hadiza tayi tashigo ta kunna wuta dakin yayi haske takalli Nura tace “kanka akeji daman sabida Mama tamin fada ne nazo turakan ka amman jibi yanda ka wulakanta ni, ka shanyani agado kataho dakin danka zaka kwana anjima kahau cewa ban maka komi na aure, oya kajika gabanka aruwa kasha mana kasan ai ka iya biyo sahu idan jarabanka yataso maka ka lallabani nabaka, ina jiran ranan zakasha mamaki na nima wlh” tajuya fuuu tafice daga dakin ta bugomusu kofa saida Aman ya firgita cikin bacci dasauri yarike Aman yana patting head nashi, chan bayan yakoma bacci yatashi yakashe wuta yadawo ya kwanta yayi bacci abinshi. ** Washegari normal aikinta Ummi tayi Hadiza tasauko tai breakfast around 8 tawuce tafita abinta ko biyar bata bawa Ummi ba dan ba son tafiyan takeba, saukowa Nura yayi yana sanye da wata farar shadda yayi kyau bana wasa ba har gaban dakin Ummi yaje yayi knocking bude kofa tayi chak numfashin shi ya tsaya ganin Ummi tana sanye da sabon black dogon rigan daya saya mata, ta tsife kanta jiya da daddare ta wanke da sabulun wankanta abinta ta taje tayi Parking batada cikan gashi at all dan kanta ma small head gareta amman wani kalan coily blonde-black hair gareta dan gashinta ba baki sidik bane irin jajajan nan ne orange orange baki baki, fari fari irin gashin agwai haka gashinta yake ta yana gyale akai daya dan ja baya tasa kwalli a idanunta, rigan yamata chass ajiki ganinshi dan tun jiya sai yanzu suka hadu yasa ta juya dasauri zata koma cikin daki karaf yakamo hannunta dasauri tajuyo suka hada ido ta zubamai fararen idanunta dasuka sha kwalli ta diga kwalli in between giranta guda biyu tayi wani kalan unexplainable kyau, ahankali yasaki hannunta dayaji yamai taushin gaske kaman yarike hannun Amal sai kawai yajuya dasauri yayi dinning dan rabon dayaji wani abu yatadamai da sha’awa harya manta, ganin Ummi da dan kama hannunta dayayi just awaken libido nashi zama yayi a dinning yayi crossing leg da sauri batare daya juyoba yace “kin gama hada komi ina gama breakfast zamu wuce” daga chan ta dakinta tace “eh nagama” itama komawa daki tayi dasauri yanda taji hannun Alhaji cikin nata sai taji tana fitar da numfashi kashi kashi. Tass yayi lafiyayyan breakfast sannan yazo wajen kofan yace “kawo kayanki mutafi” bude kofa tayi rike da ghanamasgo dinta akunyace kallon Ghanamasgon yayi sai kawai yajuya yace “ina zuwa” sama yakoma yadauko babban suitcase nashi yakawo har gaban dakinta ya duka yabude ya karbi Ghanamasgon baiji kunya ko kyama ba da kanshi yabude yashiga jera mata komi a suitcase din, yarinyar nada tsafta dudda kayanta sun mutu but komi awanke alinke ga dan black leather dayakai hannunshi zai taba dasauri Ummi ta duka tarigashi dauka hakan yasa ya kalleta sai kawai yayi murmushi dan yasan menene turawa tayi akasan akwatin nan da nan yagama hadawa suka kulle yaja akwatin waje Ummi na biye dashi har mota gaba yau yabude mata yana kallonta shiga tayi ahankali ta zauna yakallulle yadawo gaba shima yatada mota har Gwarimpa bakaramin addu’a Hajiya tamusu ba sannan Meena da Baffan shi da ita suka tafi airport ga mamamkin Ummi abokanshi tagani a airport already suna jiransu da Musa da engineer sunci manyan kaya sai kallo Ummi suke munafukai saijin dadi suke, jirgi suke shiga kalan tsoron da Ummi taji a ko tadauka mutuwa zatayi haka sukakai Yola motoci taga suna jiransu guda daya daya security personnel sauran nasu nan aka dauki hanyar kauyensu though sun tsaya a hanya anyi sayyaya na ban mamaki kayan abinci shopping da sauransu. Tunda Ummi taga sun dauki hanyar kauyensu gabanta ke faduwa hannunta suka fara rawa komi nadawo mata sabi fill Hannunta Meena tarike tace “ga dukanmu, ga mopol yan sandan chan babu abinda wani katon dan daban kauye ya isa yamiki” tafiyan awa daya da rabi yakaisu kauyensu, kauye ne da yamayi developing ga government work akwai government school, burtsatsai, primary health care da sauransu sai kallon ko’ina take komi ya chanza ta dade rabonta da garin har gidansu wanda yake babban gida ginin kasa irin na da din nan. Wata tsohuwa sosai haka na zaune a tsakar gida tana mulmula hura taji ihuuu hayaniya a waje tace “Allah yasa ba shaidanin yaron nan ne yazo dawani bala’in ba yau” da gudu wata yarinyar mai kama da Ummi yar karama da bazata wuce 13yrs ba tashigo tana hakki. “Gwaggo Gwaggooo Ummi, Umm…..” kafi takarasa magana Ummi tashigo gidan tareda Meena, mikewa tsaye Gwaggo tayi saikuma tasa zani ta murje idanunta tasake kallon Ummi data tsaya tana kallon Gwaggo, Gwaggo tace “Kodai mutuwa ce tazomini yasa nike ganin kaman Ummi achan tsaye dawata balarabiya” dawani kalan gudu Ummi tazo tafada jikin Gwaggo sai kuka ga kanwar Ummi ta biyun itama tashigo sai kawai dukansu sukahau kuka dagota Gwaggo tayi tace “Ummi kene binni ya karba haka kin ganki kuwa ya akayi kikazo? Banace kada kizo ba duk sati sai Mudi yazo gid…..” fuska Ummi ta share tace “Gwaggo akwai baki maza awaje dauko tabarma Aisha ki shimfida wajenki zukazo” dasauri Gwaggo tace “bakin yan uwan baturiya nan ne, yaki yarinya gaki fara kaman madara” murmushi Meeena tayi tazo ta gaida Gwaggo, Gwaggo ta aika Aisha ashigo dasu nan da nan aka shigo dasu wai bakin Gwaggo yaki rufuwa taga manyan dattijawa ansha shadda fura tashiga hada musu kowanne a kwarya mai kyau su Aisha harda Ummi dama Meena natayasu har Baffa saida yasha huran sun dade basu sami aslin ingantaccen fura irin wannan ba sukai salla. Daukan nasu huran sukayi su Ummi duk suka tafi daki saida aka gama Baffa ya gabatar da zancen daya kawosu wai Gwaggo kasa boye farin cikinta tayi nan ta sanar dasu komi game da Ummi da aurenta ada tace zancen aurenta kuma maigari ne mai bada yaran aure Dan haka atafi wajenshi nan akanshigo da komi aka shiga mota aka tafi wajen mai gari shima yayi naaam babu wani wahala Dan Auren bazawara ba wahala and tanada right Ummi tafito da mijinta yanzu tunda nabiyu ne kuma itane takawoshi har kauyensubnan da nan su Musa suka ijiyema abokinsu sadaki dubu dari uku aka daura aure tsakanin Nura da Zainabu Ummi akan sadaki 300k mutane dayawa sun shaida aka kawo su goro cingam menene menene aka rarraba wai Nura sai murmushi yake he just can’t believe it duk suna wajen Aisha tazo da gudu tace “Gwaggo ga Mudi chan yazo amman yan sandan nan sunmai duka” tashi Nura yayi da sauransu Maugari yace “dan Allah kukai yaron nan gidan yaro ya addabi mutanen Hm kauyen nan” komawa sukayi akai arresting Mudi nan fa Gwaggo tayi throwing small party itadai Ummi taja makale adaki taki fitowa Meena ko tafito sai video take yanda matan kauye ke rawa Musa yakawo bakinshi saitin kunnen Nura yace “kai mutumina bura’uban chan haka kauye keda tsala tsalan mata bazanyi wuff dawata ba kuwa anan kai jibidai kirjin wanchan dake rawa” tureshi Nura yayi yace “dan iska” dariya Musa yayi yana kallon yammatan, Musa yataba engineer yace “kaga yara amman Allah yamusu kindirmo a kirji” Nura yayi kaman baijishi ba aranshi yace “na Matata Ummi tamafi kowa nan kindirmo” yadan lashe lips yana kallon agogo, Aisha ne tazo tace “Gwaggo tace kazo” binta yayi zuwa falon Gwaggo tana zaune ga Ummi agefe kanta akasa zama yayi ahankali Gwaggo tace “Nura na yaba da hankalinka ne saisa nabaka Auren jikata dan mutumin kwarai ne zaisa diyarka a mota da yan uwanshi azo har kauyenku a nemi aurenta dan haka nabaka ita amana kagansu nan su hudu ne dukansu marayun Allah ne ba uwa ba uba kaji tsoron Allah bamu da kowa a binni dazance je gidan Ummi dobamin ita, tana hannunka ka kulamin da ita na yarda da tarbiyan dana bama yaran nan sunada kunya natsuwa amana da girmama na gaba dasu Ummi bazata taba cutarda kai ba Ummi matace karike ta amana sai kuma inaso nadan roki alfarma ka barta tadanyi ko sati guda ne anan wajena a danyi mata gyaran amare” abu Nura yaji ya tsayamai awuya Gwaggo tace “kayarda”? Ahankali yace “ba matsala” Gwaggo tace “yauwa tunda an kama shegen yaron nan banda sauran tashin hankali na gode Nura bari nafita nabaku guri kuyi sallama” Gwaggo ta tashi tafice. Juyoda kanshi yayi yakalli Ummi da kanta ke kasa tana jikin bango kaman ruwa ya hadiyeta mikewa tsaye yayi yana duba agogon dake daure da writs nashi sannan yakalleta yace “tashi ki rakani Amarya zan tafi” akunyace Ummi tadaura duka hannayenta kan fuskanta tarasa inda zatasaka kanta sabida kunya, he loves yanda takemai yarinta yarintar nan kunya kunyan nan, gently ya duka agabanta dab da ita yana kallon dogayen yatsunta masu fararen kumba dake kan fuskanta daya rufe yayi shiru, kamshin da Ummi taji na shiga hancinta yasa tadan ware two of her right fingers kaman munafuka tadan bude idanunta dan so take taga ina yake dan yanda takejin kamshin turaren nan nashi karaf suka hada ido ya leko fuskanta ta spice na yatsun ahaukace ta yunkura zata tashi karaf yariketa hannunshi daya yakai ta waist nata yarikota dasauri taboye kanta akirjinshi sosai takejin kunyanshi, yanda yaji fuskanta akirjinshi yasa ahankali yasaki hannunta yakai dayan hannunshi daman bayanta yaturata tashiga kirjinshi gabaki daya sannan yacire hannunshi daga waist nata yasa dukansu abayanta ya rungumeta da kyau tareda sauke ijiyan zuciya ataushashe yace “Assalamu Alaykum Matata Zainab” wani irin sanyin kunya Ummi taji tanaji takasa yarda jikin Alhaji take arungume haka, wlh kirjinshi bala’in taushi ga fadi kaman wani katifa, tun tanajin kunya taki sakin jiki hartai lamo tadaina motsi tanaji yanda kirjinshi ke beating ahankali, wayanshi ne yahau ringing batare daya saketa ba yazare hannunshi daya yaciro wayan yakai kunne Ummi bataji akace ba, amman da muryanshi dataji harya chanza launi yace “bari nagama sallama da iyalina nafito” yana maganan yacire wayan daga kunnenshi yamaida aljihu kafin ahankali yakai hannunshi daya yadago kanta daga kirjinshi maida kanta tayi da sauri, murmushi yayi cikin whispering yace “ina sonki Ummi, amman banji amsan soyayyata aranki ba aka daura mana aure kina sona”? Noke kanta tayi akafadanshi kaman yanama yarinya magana yace “kunyana kikeji?” Gyadamai kai tayi, ahankali yace “nazama mijinki yanzu babu ragowan kunya, yaushe zaki bani amsa?” Kanta yasake dagowa for the second time wannan karan batai musu ba ahankali ya manna mata peck agoshi batare daya cire bakinshi akan goshinta ba yace “zanbar miki Meena da some mopol anan ranan itiyau zan dawo na dauke, banda yawo, idan kinason wani abu ki kirani ki sanar dani kinji”? Gyadamai kai tayi ahankali yasa hannunshi a aljihu yakamo soft hannunta yasa bandir na 500 aciki yace “ki ijiye kudin nan tare dake kome kikeso kiyi dashi kinji”? Gyadamai kai tayi, har lokacin bakinshi nakan goshinta lips dinta ya kalla tanada a bit chubby soft bottom lips sai na saman is slightly thin a bit pinkish a bit dark he seriously wanna kiss her like right now but then yanason tazama comfortable dashi dan ijiyan zuciya yasauke kadan kafin ahankali yasaketa yace “zan tafi” dan komawa baya kadan tayi kaman kada tafita daga jikinshi tana sussunnar dakai tace “Allah maidaku gida lpy nagode da abubuwan daka kawoma su Gwaggo Allah kara budi mai albarka” Ameen yafadi yayi wajen kofa dan juyowa yayi yakalleta kaman yadauketa yakeji yadai daure yadaga labule yafita daga dakin. Bin dakin Ummi tayi da kallo ganin littafai da byro akan wani dan table yasa taje wajen ta bude tsakiyan book yafalllontahsiga rubutu, dasauri take rubutun cikin 2min tagama tadaga takara karantawa sannan tashiga linke paper wani kalan linki tama paper kaman flower wow yarinyar is creative fitowa tayi daga dakin da sauri Aishan su tagani tabata tace “imaza kaima mijina Shatu maza kafin su tafi” da gudu Aisha ta fanfala sai alokacin Ummi tadaura hannunta kan bakinta jin tace mijinta, Aiaha nafita suna tafiya haba tabi motan da gudu tana ihu yaran anguwa suka bita suna tayata ihu ana. “Mota ku tsaya ku tsaya” abunku da yaran kauye, Musa yafara hangosu dasauri yace “Nura wanchan ba kanwar Ummi bace ke biyomu da gudu da tawaganta” lekawa Nura yayi ganin yanda yara ke gudu ana ku tsaya yacema driver ya tsaya parking sukayi da gudu su Aisha sukazo wajen 𝕄𝕦𝕤𝕒 dasauri yabude kofa dan daga Nura sai shi sai engineer Baffa na dayan motan, ana bude kofan Aisha da karfin muryanta tana haki tace “Yaya Ummi tace nabawa mijinta wasikar nan” tamikama Musa wasikar juyawa Musa yayi yakalli engineer dake murmushi sannan Nura daya hade rai Musa yamika hannu yace “to sannu da aiki Shatu kawo” hannu yasa zai amsa saiga hannun Nura ya fizge ya sa a aljihun gaban riga yabama yaran wasu kudi daya ciro daga aljihu yace “nagode” yaran suka kwasa aguje Musa yarufe kofa yace “jamuje direba” yakalli Nura yace “wowww Ango wlh soyayyan kauye tayi ne jibi wani wasika da aka aiko maka an mata wata kinmin fulawa kaga engineer billahillazi a kauyen nan zanzo nima na nemi amarya inaaa kai kaga yaransu ne sunsha kindirmo tun suna jarirai yanzu duk yakoma kirjinsu” dariya duk sukayi Engineer yace “kaidai kwarto ne Musa shegen gari, kai ranan kasa na kusan kashe madam wannan maganin basir ai bala’i ne” dariya Musa yayi suka cigaba da hira ganin haka yasa Nura yaciro wasikar yana yaban design da magic na maida sheet of paper into flower shape da Ummi tayi ya warware ahankali. “Assalamu Alaykum Baban Amalily, wanda yazama mijina ayau rana uku ga watan maris. Amsan tambayan kace awannan sakon” Gyara zama Nura yayi yacigaba da karatu. “Acikin wani bakin dare mai duhun duhu daban taba tunanin zanga haske awannan daren ba wani haske ya gauraye inda zuciyan Zainabu Ummi take, kasan haske nada zafi a ido dakuma fata sai wannan hasken ya kasance mara zafi, mai taushi ce dakuma da tsantsa kyawu, kyawu irin wanda bantaba sanin akwaishi ba awannan duniyan sunan hasken nan NOOR wato NURA! Ana haka wata kalan guguwa mai karfi ya taso dake dauke da kifiyoyi guda uku masu zafin rabasheshen dalman wutan kauna ce ke tashi daga jikinsu, suna zuwa chak! Chak!! Chak!!! Suka sossoki zuciyata, kifiyoyin nan guda uku na dauke da kalma guda uku ne na farkon yace I nabiyun yace LOBE na ukun yace YOU!!!, I lobe you My Noor Baban Amalily” Yihuhuuuu!!! Nura yabuga ihu kaman dan daba dayasa su Musa duka suka juyo suka kalleshi yace “wlh Yarinyar nan ta tashi kaina, billahillazi dauko matata zanyi, kai dereba juya kan motan nan kaga ku kusauka ku shiga dayan motan, ba’a taba gayama Nura irin wannan kalaman soyayyan ba, wayyoo zuciyata nima kifiyoyin dalman soyaya sun chakeni” tsayawa duk sukayi suna kallon Nura kaman kanshi ya kwance. Hahahahah Guys rate sakon soyayyan yan kauyen M shakur naku, I crafted this on my own chaiii yayi making sense kuwa???😂😂😂😂😂 Ummi fa zata haukata mana Nura Hadiza sorry for you, just look at how Ummi ke feeding mijinki soyayyan kauye, soyayyan uneducated girl. 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 8️⃣ Adan birkice direba ya gangara zuwa gefen hanya yayi parking yin yanda Nura yabuga ihu, Nura yana murmushi sosai kaman wanda yaci lottery yakalli su Musa da duk suke kallonshi asankare irin ikon Allah din nan yace “kufita mana” dasauri Musa yace “ohhh Allah kana gwadamin halin Nura yau kaine haka kake rawan jiki kaman wani sabon shiga? Shekaran ka nawa yanzu kana buga odafere”? Kwashewa da dariya Engineer yayi yace “kai wlh dan iska ne Musa, mekuma Odafere” yakalli Nura yace “dan Allah kayakuri mutafi Nura, mukoma Abuja this one week Musa ya loda maka maganin basir kaga system dinka yayi refreshing afitar da toxins din ciki, sabon ruwa yazo yataru a buhu” dasauri Musa yace “itama bakasan da Gwaggon nata tace abarta abinda za’a mata ba kenan duk dadin kane fa, gyaramaka ita za’ayi fa, kuma ma ai da kunya kawani koma saikace wani saurayi, kawa Allah ka rungumi letter nan yarage maka zafi mutafi kai direba tada mota next week fa karenka zakaci ba babbaka” tada motan direba yayi badan yasoba yahakura cus yasan gaskiya suke fadi, koda suka shiga Abuja gidan engineer yaje yaci abinci yayi knack sukasha hira wuraren 11 yabaro gidan yakama hanya suwa gudanshi yakira Ummi amman wayanta akashe maybe ba chaji baiso yakira wayan Meena kuma around 11:30 yashigo gidan, yana bude kofan falon yasan Ummi bata gidan yau kaman ba falon da Ummi ta gyara dazu da safe ba. Dakin gabaki daya a hargitse, school uniform din su Aman na nan falon da jakunkunan su da safa, dinning hargitse da plates ga ragowan abinci indomie yagani da egg is as if yaran basuci ba gadai cups na tea da ragowan slice bread da alamun abinda sukaci kenan, kitchen yaleka daganan dinning just indomie da Hadiza ta dafa tajuya kitchen din up side down kaman ba kitchen din daya shiga ya zauna aciki bane harya sha shayi rannan da Ummi ba, ijiyan zuciya yasauke yadawo falo da kanshi ya duka ya tattare kayansu na school sannan yabude baga nasu yaciro books nasu sunada homework ba’ayiba and wlh dudda Ummi is uneducated she manage ta koya musu homework duba ayyukan su nada yayi da Ummi ke tayasu duk sunci to menene ma amfanin auren Mai ilimi tunda bazata iya yima yaranta homework ba, kwasan komi yayi yawuce sama yakai kayan kowa dakinsu yana kallon yaran da ba’a musu wanka ba normal kayane ajikinsu bana bacci ba da Ummi tasaba saka musu, shiru yayi yanzu haka yaran nan zasuyi rayuwa, shi karan kanshi bazai iya kwatanta yanda yakeson yaranshi ba bazai dauki rashin kulan nan ba da rashin basu abincin nan ba ko kin musu homework ko uniform ma sabida yasan sunada wani set dazasu saka gobe ne amman what’s all this dakinshi yatashi yatafi yaje yayi wanka. Da asuba as usual yafito harzai wuce yasauka kasa saikuma yajuyo dan yayadata tama yaran nan abincin school ta shiryasu gaban dakinta yaje tareda bude kofan yashiga ya kunna wutan dakin, bauu dakin yayi haske yatsine fuska Hadiza dake lafiyayyen bacci tayi jin haske, tadan bude idanunta kadan ganin Nura yasa cikin muryan bacci tace “Nuri am off salat ka tafiyan ka masallaci basaika tasheni ba” yana daga wajen yace “get up fix something for the kids and get them ready for school sannan basuyi home task nasuba, and arrange the house yayi datti gidan” wani kalan ware idanunta Hadiza tayi tasss takalli sama saikuma ta tashi zaune da sauri ta kakkalli gefe da gefenta dan she wanna be sure cewa bada ita Nuri yake ba ganin bakowa adakin yasa tanuna kanta da sauri tana kallonshi cikeda mamaki tace “Nuri ni kake bama order haka kake lissafo ma ayyuka haka?” Duk yanda taso kasa rike dariyan datakeji tayi tadan kyalkyala dariya tana nuna kanta tace “wait are u mistaking me for Ummi ne or wat dakake lissafo mini abubuwan da zanyi, idanunka gizo suke maka ne Nuri? Nayi kama da yar aikin mu ne? Wait ma kai what happen da u can’t do all of this abubuwan nan daka fadi are you not mahaifinsu? Can’t u cook for them? Can’t you bathe them and get them ready for school? Bazaka iya musu homework nasu ba? Who said shirya yara, basu abinci, getting them ready for school da gyaran gida responsibility mata ne kadai?” Babu wasa kan fuskan Nura yace “ki tabbatar kin tashi kin soma aikin dana fadi kafin nadawo gidan nan daga mosque” yana maganan yajuya yafita daga dakin mamaki yasa Hadiza tama kasa zama tashi tayi dasauri tasauko daga kan gado tafito daga dakin tabiyoshi abaya tace “Nuri ni kake commanding like that are you for real? Kalleni fa” tanuna kanta tana sanye dawasu arnaye kayan bacci tace “do I look like a house help? Listen fa Nuri lemme tell u something ko Allah yasan ni ba housewife bace, I have a business danake managing, I contacted agency masu kawo yan aiki babu wasu akasa za’a nemo mini, idanma zaka zauna and be attending to this children reschedule work naka do it tunda Ummi tatafi garinsu dankai ur company is big kaine CEO kanada manager dazasu iya managing komi niko banda manager, I manage everything about business dina nikadai banda sales girls danake dashi dake attending to customers namu but I do komi dakaina dan haka Nuri attend to ur kids, babu inda aka rubuta a musulunci cewa dolen dole mama ce zata dingama yara komi yaran nan na me and you get them, gaskiya I don’t have that tim…..” ganin Nuri yabude kofa yafita yasa Hadiza ta tsaya turus da mamaki, Nuri just walk out on her tanamai magana irin baida lokacin ta wow! Tana kallon kofan kirjinta na tafarfasa, da tayi niyan ko falon ne tadan tattare suyi sharing work din amman wlh tafasa tayaya zaiki girmamata ita ta girmamashi, wani disrespect ne hakan? Wannan sabon confidence din da Nuri yake mata kodan sabida yaga yasaketa tadawo gidan da next day ne yasa yake mata Iskanci haka, ta inama zata fara all this ayyuka Allah ma yasan bazata iyaba wlh, rabon datayi aikin gida harta manta to tariga tawuce wannan level din nayin aiki dakanta agidanta Allah ma yasani, idan tayi aiki agidan mijinta menene banbancin gidan ubanta da gidan mijinta? Kana gidan iyaye ne u must work, abaka umarni kabi, but your husband house suppose to be your paradise that’s the beauty of aure, kiyi duk yanda kikaga dama agidanki, kici karenki ba babbaka, tanada kudi mijinta nada kudi maisa zata tsaya da kanta tana all this silly household chores? No Nuri u can’t subject to into doing abinda zuciyana baiso yayi, itama shegiyan yarinyar nan akan wani dalili zata sakani in this tight spot, that stupid Ummi datawani tafi shegen kauyensu wai wajen kakanta, juyowa Hadiza tayi tarike waist nata tabi falon da kallo yanda yayi datti ga kwanukan abinci tsaki da ragowan food a dinning tayi tai ihuuu. “Wayyyooooo, Goddddd! A ina zan sami yar aiki yaune ni Hadiza? Ohhhh I can’t do this, how can I start doing this chores haba dan Allah, ai abin kunya ne, niba yar aiki bace ba I can’t do this wlh, ni nama manta yaya ake girki ma, indomie nan koni nakasa ci dana dafa jiya ewww, yuck” ta yatsine fuska, komawa sama tayi dakinta tawuce bayi abinta. Dawowa gidan yayi around 7 yanda yabar falon haka yazo yasami falon sama yawuce Aman yagani da Amal duk sun zauna anan falon sama sunyi zugum kaman marasa lafiya, ganin babansu dasauri suka tashi sukai wajenshi Aman yace “Dady where’s Anty Ummi”? Amal kuma sai kawai tafashe da kuka tace “Daddy ina Anty Ummi tun jiya banganta ba she’s not in her room” tausayin yaran yaji dasauri yadauki Amal yakama hannun Aman yawuce dakin Amal yarufo kofa yace “Anty Ummi taje garinsu amman zata dawo next week I promise” dasauri Aman yace “daddy ka kaimu wajenta” shiru yayi yana kallon yaran saikuma yaga sun fashemai da kuka dukansu biyun atare dasauri yashiga lallashin su wayanshi yaciro yayi dialing number Ummi yana addu’a Allah sa akunne, kafinma wayan yayi ringin Aman ya karbi wayan yahau kan gadon Amali itama Amal tahau gadon kusa da Aman ta zauna wayan na ringing daya biyu Ummi tadauka cikin sweet voice nata data wani lankwasa ganin number mijinta tace “hello” atare yaran sukace “Anty Ummi” saikuma suka fashe da kuka atare, cikin kuka Aman yace “why did u go to kauye baki gayamana ba”? Amali tace “bakince zakije damu duk randa zaki kauyeba” Ummi jitayi zuciyanta ya tsinke dasauri cikin dabara tace “Aman wait one by one” a cartoon nasu ta koyi kalman, cikin kuka suma yaran sukace “one by one” ahankali tace “Aman daina kuka bari nafara magana da Amal” gyadamata kai yayi kaman yana gabanta cikeda lallashi Ummi jin yanda Amal ke kuka sosai tace “Amalily na, Amalily Dadynta, Yarinyar datafi duka yaran duniya kyau, ga gashi, gata yar fara, baturiya, balarabiya, Princess Amal Nura Wambai ammatana” wani kalan murmushi Amal tayi tana turo baki da saida abin yasa Nura yasaki baki yana kallon ikon Allah yarinyar dake kukane yanzun nan hartai murmushi sabida taji kirari ana cemata Ammata wai tafi duka yaran duniya kyau, gyara zama yayi yana kallonsu cikeda so. Ummi tace “banson Mudi yagane mini ke ne saisa ban gayamiki ba nazo amman zan dawo next week zan kawo miki goruba da aduwa da hanjin ligidi” dasauri Amal tace “tuwon madara fa”? Dariya Ummi tayi tace “harda tuwon madara Amal dina” wani ihu tayi tana tafi Ummi tace “tom jeki brush ba Aman wayan” bawa Aman wayan tayi tasauka dagudu tawuce bayi Ummi tace “takawanka lafiya d’a guda kuma daya tilo ga Baban shi, Mr Aman gogan zamani, matashin saurayi, dogo, yaro ga ilimi ga tausayi, yaron dayafi kowani yaro jin magana da hakuri kaman Baban shi, Amanu Aman babban yaya ga Amalily, haba ama Anty Ummi hakuri mana eh Yaya Aman” dan turobaki Aman yayi yana murmushi sosai yana juya idanu looking super cute ahankali yace “to nayi amman idan kinzo zaki mini Oumu Oumu mai cheese a tsakiya” dasauri Ummi tace “zanyi” murmushi yamata yace “bye bari naje nai brush” yana maganan yabawa babanshi waya yatafi bayinshi cire wayan Nura yayi daga Speaker yakai kunnenshi yadan lumshe idanu yace “nikuma mezan samu nida nafi kowa yin hakuri”? Dan murmushi Ummi tayi cikin wata narkakkiyan murya tace “barka da safiya Baban Aman da Amalily mijin Ummi kuma, ina kwana My Noor” wlh ko baitabajin sanyin dayakeji irin wannan dayakeji ba da gaisuwan nan datamai sai kawai yaji kanshi na kumbura, ahankali yace “Alhamdulillah ya darenki? Yasu Gwaggo? Meya sami wayanki jiya akashe” “Kowa lafiya lau, ba chaji ne, ya jikin Hajiya kuma yau zakuje asibiti?” Gyadamata kai yayi yace “eh zanje nakaita taga Dr” murmushi tayi tace “tom bari na barka kaduba Amal nasan wasa da ruwa take yanzu haka” dudda baiso ba haka yace “to zan kiraki anjima, kema kije kiyi breakfast, agaida mutanen gida” to katse wayan yayi yatashi yawuce bayin Amal shiyama yaran wanka ya shiryasu yadauki akwatin su yazuba musu kaya aciki komi dasuke bukata, yajawo suka fito falo Hadiza na zaune afalo taci uban gayu tasaka hill takada ma kanta tea tanaci da bread kadai anan kan kujera ganinsu duka da akwati yasa tace “ina zaka kaisu naga akwatinan su”? Batare daya kalleta ba yace “inda za’a kulamin dasu tunda bakida lokacin su” kofa yayi tabisu da kallo yaron ko kallonta basuyi ba, saikuma ta tabe baki ita adadinta ma atleast yau zatai zamanta ashigo without tunani su, amota ya lodasu straight gidan Baffan shi yayi dan Hajiya tacema yakawo su nan dan da ita ya tsaya yayi magana awaje kafin ya shigo gidan, akwai kananun yara agidan, anan sukaci abinci aka zuba musu abinci a lunch bag nasu dakanshi yakaisu makaranta sannan yabada addres na gidan kan anan zaa dinga zuwa daukansu sannan yadawo yakai Hajiya hospital. *** Kusan 2min Meena tayi adakin da Ummi take zaune ga roban farfesun zabo agabanta bama ta taba ba tayi nisa sosai tana tunani, dan ijiyan zuciya Meena tasauke ta duka ahankali ta ijiye kofin madaran shanu mai zafi dake dauke da magani da Gwaggo tabata takawoma Ummi ta ijiye agabanta sannan ta taba Ummi tace “Ummi” firgigit Ummi takalleta tace “Na’am sorry banjikibane Meena” Meena dake kallonta tace “tunanin me kikeyi haka Ummi? Kinsan sau nawa ina kiran sunanki baki jiba tunanin me kikeyi haka?” Dan shiru Ummi tayi takasa magana hakan yasa Meena tazauna da kyau agabanta tana kallonta tace “meke damunki Ummi?” Yanda Meena ta tsareta da idanu yasa ahankali tace “Meena bansan yaya zan kalli Anty ba, bansan yaya duniya zata kalleni ba nazo aiki na aurema mata miji, kawai jinayi banajin dadin dan kaman nayi cin amana ne, wani kalan rashin jin dadi nakeji azuciyana da damuwa dadai wani iri” ahankali Meena tace “shi ake kira da guilt” ahankali Ummi tace “inajin shi guilt din azuciyana sosai wlh” ganin yanda Ummi tayi yasa ahankali Meena takama hannunta tace “Ummi tsaya kiji abu na farko danake so nafada miki shine Matar mutum kabarinsa, inhar Allah yarubuta wane ko wance matarka ce saika aureta ko ana k’ak’a” hannunta Meena tasaki tace “nasan yanda za’a kalli abin amman bakida laifin komi a case din nan” dan shiru Meena tayi saikuma ta nisa tace “Ummi kinga Yaya Nura bantaba ganin namiji Mai kirki da bala’in hakuri da rashin magana irinshi ba, tun yana yaro haka yake, baida hayaniya, baida rigima, baida fada, dukanmu kanninshi mata ne dukanmu mun taso shike kula da mu, ya wanke mana kaya, har yau ina tuna yanda yake wankemin kashi da ina yarinya yamin wanka ya goyani, ba karamin taimakawa Hajiya da rainanmu yayi ba cus tun ina yar yarinya babanmu yarabu da Hajiya sai Ya Nura yazame mana uba, wannan dabi’un nashi na sanyi da hakuri yasa Hadiza ta matukar rainashi” Meena tasake sauke ijiyan zuciya tace “nasan kalolin dumbin tunanin dakike azuciyanki Ummi irin yaya zakiyi kiyi zaman kishiya da Anty Hadiza, bari kiji aure is not about how beautiful you are, ba kyau, boko, kudi dawasu ado da kyalekyalen duniya bane aure ba dan duk zasu iya karewa, hali shine aure, halinki amatsayinki na mata zaisa mijinki yaji yana bala’in sonki da girmamaki haka kuma shi wannan halin shi zaka mijinki yaji kin siremai yakuma gaji dake, and duba ga abinda ni nagani da idanuna Ummi halinki da dabi’unki yasa Yaya Nura yakamu da sonki kaman yanda aranan damuka shigo Abuja muma mukaji muna sonki” Meena takai hannunta saman kan kafadan Ummi tace “ki cigaba da halinki abinda ake cewa da turenci keep being you Ummi, the caring sweet and soft Ummi mai kulawa da kowa, ki tsarkake zuciyanki ki shiga gidan Ya Nura da zuciya daya kiyi zaman aurenki kada ki bari wata ta zageki ko taci miki mutunci dagake har ita duk zamanshi kuke, wannan kunyan ki ijiyeshi agefe Ummi kinfini sanin abubuwan da Ya Nura baya samu wajen matarshi ke kibashi dan kin zauna agidan dasu, sannan namiki alkawari zan baki wasu abubuwa karatun classes na matan aure da M shakur keyi da hausa dan kowa yagane ki karanta sannan zan biyamiki kudi ki shiga classes din kokuma ma zan biyata ko nawa zata chajeni tamiki private erotic hausa class dantanayi ma wayanda basason group, ki koyi abubuwa ki ijiye kunyan nan ki farantama mijinki sama da yanda yar birni wayayya ma zata iya, ke ba budurwa bane kin Riga kin wuce level din nan, ba wani kwana kwana ki shayar da Yayana dadi da kwanciyan hankali and kiso mijinki sama da komi is not a crime kinji” Gyadamata kai Ummi tayi ahankali tanajin wani kalan kwarin guiwa Meena takai hannunta ta share mata dan guntun hawayen daya zubo tace “maza saki jiki kiyi walwala kisha magungunan ki da kyau ana miki gyaran jiki dan ki mantar da Yayana damuwanshi kuma ba kunya ehe kinajina” akunyace Ummi na murmushi ta sunnar da kanta dariya itama Meena tayi tanason kunyan Ummi ta tashi tafita, kofin Ymmi tadauka tafara sha saikuma ta kalli wayanta kewanshi kawai taji tanayi wlh ahankali tadauki wayan dailing numbershi tayi Kunya kuma saiyasa ta katse dasauri daga aurensu jiya dazu kuma yakirata dasafe saitayi ta damunshi ijiye wayan tayi agefenta dasauri tadauki cup din zata sha wayanta yahau ringing dasauri takalli wayan ganin shine yasa takai wayan kunnenta asanyaye tace “ina yini” cikin murya kaman batasaba yace “lafiya lau Ummi na kewana kikayi kikemin flashing”? Rufe fuskanta tayi kaman yana wajen baki tabude zatace a’a murya ciki ciki tace “eh” dasauri tazaro idanu taredakai hannunta ta rufe bakinta saikuma da karfi tace “wayyoo Allah ni a’a fa zance nace eh” hahahha Nura ya kyalkyala dariya wani kalan dadi yaji bana wasaba yanda she’s missing him din nan, cikeda so yace “kada kidamu nakusan zuwa na daukeki nima nagaji wlh kewan Hajiya Ummi nake sosai” adan kunyace cikeda son abar maganan tace “kaci abincin rana? Kun dawo daga asibitin da Hajiya ya jikinta”? Dan shiru yayi ko Allah yasan yanason yanda take tambayan jikin mahaifiyanshi da yanda take tambayan yaci abinci cikeda so yace “naci abinci tareda Hajiya Ummi, munje asibiti taga duka tests nata sun fito Dr yabata magani zatasha na 2weeks saimu kara komawa” dan ijiyan zuciya Ummi tasauke tace “Alhamdulillah Hajiya zata warke kaman ba itaba in sha Allah tayi ta tafiya da kanta batare da taimakon wani ba, akwai wani mai da Gwaggo tabani dana gayamata wai tadinga shafawa akafan zasuyi sauki” murmushi yayi yace “bari naduba jirgi nazo na amsa” dan zaro idanu Ummi tayi tace “aikin fa”? Yana murmushi yace “zan ijiyeshi agefe nazo naga matata wai nazo na amsan ma Hajiya maganin ta” kyalkyacewa da dariya Ummi tayi dayasa yayi shiru yana sauraran dariyanta dakema kunnuwanshi dadi kaman busan algaita, ahankali yace “ina sonki Ummi, Nura na sonki” akunyace ta sunnar da kanta tana boye kanta acikin guiwanta tana dariya kasa kasa hakan yasa murya chan kasa yace “bazaki gayamin kina sona ba? Maimaita abinda kika fadamini a wasikar nan” lankawshemai kai tayi saikuma ta kwanta anan kasan dakin datake ciki ta lumshe idanu kawai shitake gani cikeda shauki dakuma sautin wake dawani irin taushashiyan murya tace “banjin zugar kawaye a soyayya kaina dauka, ka sharemini hawaye, kasa nadaina kuka, indai ina araye Sam bana gudun ka, Allahu ya kiyaye banison waninka, kaine dai daya, acikin zuciya, mai sakani dariya sannu masoyinaaaaaaaaa” “Ummiiiiii haka kika iya wakan soyayya”? Cewan Gwaggo datagama jin komi, dasauri Ummi tace “wayyo Gwaggooo” ta katse wayan tana boye fuskanta bakaramin kunya taji ba ganin Gwaggo na jinta sai dariya take tana kwalama su Shatu da Meena kira suzo wakan soyayya Ummi takewa mijinta. Wallahi Nura ko at this point jiyake bazai iya ba, dudda yau anci kwana biyu kaman sati bazai juyoba haka yakeji baiso yayi abin kunya ne shiba yaroba saisa kawai yake daure wa but Ummi zata kasheshi da soyayya, watttt!!! Ba’a tabamai wakaba tun zamanin yana secondary school daya fara soyayya da all this classmate yan aji but just look at wakan soyayyan data raira mishi ga muryanta kona mawaki baijin yakai na Ummi dadi ba, tashi yaji kanshi nayi yana kumbura, abu yaji an bugamai akai hakan yasa yabude idanunshi Musa ne yashigo office din dawata katuwan jaka a hannunshi yace “waikai mehaka saikace wani saurayi sai shafa kirji kake karike waya gam a kunne kaman wanda akema wahayi, ka lumshe idanu kana cikin kogin soyayya, dalla taso kazo nan nazo na shirya abokina” Musa yayi maganan yana zama kan dogon kujeran dake cikin office din yashigan hada mishi some magunguna yace “yauwa wai ban tambayeka ba ina zaka ijiye Ummi ne? Zaka rabamusu gidane”? Girgixamai kai yayi yace “a’a bazan so yarana su taso gida daban daban ba inaso yarana su taso kansu a hade, babban gidan nan nawa nasa an fara gyaranshi kowa da flat dinta nan da 2month za’a gama aikin tass, before then anan gidana zamu zauna dakina zan cire komi naciki nayi magana dawata interior decor gobe zatazo tadauki measurement jibi za’a kawo komi, and inaso nakara siyan wani gida a Adamawa, inaso idan na daukota daga kauyensu mu zauna anan muyi hornymoon and again yarana su Aman sunaso suje kauye to irin duk ranan da zamuzo munada gida agari kagane” Musa daya bashi kofi yace “nagane but Hadiza fa kasan kar kwankwamnata su tashi ta taba Ummi fa” wani kallo yama Musa yace “duk randa tai kuskuren tabamin mata saitaga other side of me” murmushi Musa yayi yace “shegge nawa tun yanzu kafara rawan jiki haka bare kuma kasha kindirmo” bugamai filo Nura yayi yana murmushi Musa yace “Nura kalleni nan, auren nan auren hutu ne da shakatawa dakuma more rayuwanka, Allah yabaka dukiya, yabaka yara, me kake nema banda jin dadi? Matarka taki kwantar maka da hankali tunda yanzu Allah yabaka Ummi enjoy your life da yarinya danya abinka, fresh yarinyar ni irinsu Ummi I still consider them virgins wlh, to tun suna yara akai auren nan, she’s semi virgin, gata da natsuwa ga kirki, she can cook, gata she’s not expose duk inda ka juya yarinyar nan zata juyun maka meyafi haka dadi? Enjoy your self abokina our 50’s can never be boring duk wacce tace bazatai corporating ba ajiyesu kadauko wacce zata bada hadinkai kaji dadi, kagama amarci dai tukunna nima kauyen nan zan shiga na dallo amarya ita wanchan tajika farantin nata tasha tunda ta tsufa dan wlh ni ban tsufaba ina mahaukacin son farantin nan, cheers to enjoying our 50’s Nura” cheers sukayi suna buga cups na magungunan basir sha suna dariyan keta, Musa yace “wayyoo kindirmo, Nura kawa Allah kagama amarci muje kauyen nan nima na zaba na dirja, mai manyan kindirmo zan dauka” murmushi Nura yayi shima he can’t wait yasha nashi kindirmon. *** Tun ranan Wednesday Nura yashigo Adamawa, wani gida yasaya mai kyau duplex awani anguwan yan gayu da sunan Ummi yasai gidan, yashiga gyare siyo furnitures da sauransu ranan Friday gidan komi yagama haduwa dudda up and down dayakeyi baitaba missing shan maganin basir dinshi for a day ba, da kyar ya iya yayi bacci ranan Friday din nan ranan Saturday 11 yana kofar gidansu Ummi yasha wani jumper na ash yadi yasaka bakin shade da hula da takalmi yayi kyau kaman balarabe shiga cikin gidan yayi ya gaisa da matan dasuka cika gidan yabiya wasu kudaden daukan amarya da akace yabiya sannan yafito yashiga bayan jeep din dayazo dashi dan da direba yazo chan saiga Ummi an fito da ita wani alkyabba tasaka da atampa dan Nura yaturama Meena kudin tashiga cikin garin Adamawa tasayo komi, da kanta tama Ummi black and red henna takuma mata kitso Ummi harwani kyalli take abayan mota aka sakata itakuma Meena tashiga gaba, direba yaja motan, saida suka danyi nisa atafiya kaman daga sama Ummi taji yajawota ahankali yasata ajikinshi wani irin kunya taji dan akwai direba da Meena amotan kasa kwace kanta tayi tai kaman yar jaririya ajikinshi tana shakan cool kamshin turarenshi, hannunta yakarba yana kallon lallen ahankali yace “Auta wayama matana zane mai kyau haka”? Dasauri Meena tajuyo ganin yanda ya rungumo Ummi yasa tajuya dasauri tace “Yaya nine namata harda kitso ma” dasauri yace “aaah lallai Auta tai abin arziki mu bata tukuici ko baby” yayi maganan yana leka fuskan Ummi dake cikin alkyabba, gyadamai kai tayi akunyace, hannu yasa yadauki wata Prada purse dake sude na kofan motan yabude yaciro bandir daya na 1k yace “amsa Meena mun gode” cikeda dadi tace “laaaa Yaya thank you” gidan Ummi suka fara zuwa suka shiga ciki gidan yayi kyau zama Meena tayi afalo shikuma yana rikeda hannun Ummi sukaje sama daki uku ne asaman master bedroom yabude yashiga ciki da ita yana maida kofan ga mamakinta daukanta yayi chak atsorace tace “wayyoo Gwaggo” murmushi yayi yasa hannunshi ya jaye hulan alkyabban yana kallon fuskanta da black skin nata ke sheki sosai lumshe idanu yayi ya zaunar da ita kan gado tareda zama yana facing nata akunyace ta sunnar da kanta kasa, murmushi yamata yakai hannayenshi yabude boturan alkyabban yacire shi daga jikinta ya ijiye a gefe yana kallon kayan jikinta yaune first day dayake ganinta da atampa fitted daidai jikinta wanda duk aikin Meena ne ita tadauki measurement nata ta shigo birni dashi atampan yamata kyau, ahankali yakai bakinshi kan kumatunta yasakin mata peck. “Muah!” Wani yirrr Ummi taji dasauri ta runtse idanunta, batare daya cire bakinshi daga jikin kumatun ba yace “kinyi kyau sosai Zainab, kinyi kyau” idanunta alumshe itama cikin whispering tace “kaima kayi kyau bantaba ganin abu mai kyau irinka ba Noor” fuskanshi yakawo saitin nata yadaura hancinshi kan nata yana kallon dogayen gashin idanunta dan idanunta a kulle suke yace “kalleni, bude idanunki ki kalleni ki gayamini inada kyau Ummi” ahankali kaman mai tsoro Ummi tabude idanunta tahada da nashi idanunshi sun kankance kadan suna mata wani kallo da all she sees irin usulin soyayya aciki, gently tadaga hannunta daya takai saman kuncinshi wani kalan lumshe idanu Nura yayi sabida sanyin dayaji a hannnunta yakai hannunshi daya ya daura saman hannun dayaji yana rawa kaman zata dauke daga saman fuskan nashi yace “wayyooo Allah na” yabude idanunshi ahankali yadaura kan nata yace “Ummi kin iya shagaltar da namiji, wlh kina daburtamin lissafi” lumshe idanu tayi tabude su tadaura akanshi tareda huramai a very light breeze daga bakinta tace “huuuuuuhhh” ahankali ya lumshe idanunshi wani natsuwa na shiganshi yasake danne hannunta dake kan kuncinshi gam, with a vet light yet naked voice Ummi tace “tsarki ya tabbata ga Allah ubangijina, ubangijinka, Ubangijin talikai, ubangijin daya busa mana numfashi, ubangijin daya hallitoni yakuma halittoka ya halitto kowa, idanun Ummi basu taba ganin namiji da komi nashi kyau ne dashi kaman ka ba My Noor, idanunka farare fat masu asirtaccen kyau da mai baiwa irina kadai ke iya gani, fuskanka ka kyanshi zai iya sanyaya zuciyan mugu daya kawo maka hari, lafuzan ka yafi zuma zaki dakuma dadi, muryanka kaman ana busa sarewa, sarewan ma wacce ake samota abishiyan dake kan dutsen kufaina wacce take fitowa sau daya a shekaru dari, halikan gabaki daya yafi duk wani abu da Ummi tasani aduniyan mai kyau, gemun nan naka akullum saina tunashi dan shine abu na farko dake fara sanar dani zakamin murmushi” wani kalan murmushi Nura yayi yadaura bakinshi saman nata batare dayay kissing nata ba dasauri ta lumshe idanunta murya chan kasa yace “bakina kuma da kanshi zai sanar dake abinda yakeyi” soft sensual kiss yafara mata jikinshi na dan rawa kaman this is the first time yafara kiss in his life, almost 2min yayi ahaka sannan yasaki lips nata taredakai fuskanshi saman kirjinta ya kwantar tareda cuddling nata ahankali yana lumshe idanu feeling tudun chest nata kafin ahankali yakai hannunshi yaciro wayanshi, cikin muryanshi da baya fita sosai yace “wlh bazan iya kai Meena airport bari nakira direban nan yakaita”. Assalam Alaykum Ladies. This littafi ina yinshi ne dan gwadawa mata da maza some kuskure nasu, how to overcome major issues dake kashe aure and how to do and undo things a aure, I wanna ask something at this point. Kunason Erotic scene? Na koyamuku how to spice it up a bedroom? Kunason namuku erotic scene ko nabarshi??? I go with what majority want. Thank u M Shakur ✍🏻 💫 MATAN?? Ko MAZAN!??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 9️⃣ JOIN THIS GROUP DON SAYAN TURARUKA DA SAURANSU ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/Izv1KgHEcNl5uwqalMM9Oe Dialing number direban yayi yana kara manna kanshi a kirjinta but number bai shigaba yaki connecting dan malalacin tsaki yasaki yadago kanshi from chest nata yakalli fuskanta da sauri Ummi ta lumshe idanu, agajiye yataso tareda ijiye wayanshi kusada ita tareda manna mata kiss a kumatu yace “bari naje namusu sallama” gyadamai kai tayi batare data iya hada idanu dashiba tace “amata Allah ya kiyaye ta gaida su Hajiya dasu Aman da Amal, kada ta manta tabasu abinsu dana bata” dasauri yakalleta saikuma yarike waist nashi yace “wani abu aka bayar ni ina nawa”? Dan murmushi tayi yanda he always ask for nashi nabata dariya sosai saikace shi yaro ne, adan kunyace tace “iloka namusu jiya idan kana so saina maka ai but nasan bakason zaki saisa banyi dakai ba” murmushi yayi kawai yana kallonta dudda taki yarda su hada ido he loves yanda she knows so much akanshi sabida she pay attention, is this abinda yakeso yaga matarshi na paying attention to him hakan nasashi feeling special, asanyaye yace “godiya nake Hajiya Ummi” dasauri tadauki filo tadaura kan fuskanta tana murmushi, juyawa yayi yafita tadan sauke filon kadan tabi bayanshi da kallo wlh bala’in son Alhaji taji tanayi but why? Ya iya magana da ita? Yana karramata yana kulawa da ita yana nuna mata tanada daraja dakuma yanci, Komi ataushashe nashi, gashi ya iya cemata ya gode dudda ita yakamata tacemai but baida girman kai, he’s always thanking her for every little thing koda abinci tabashi, kwata kwata yanda yake rayuwanshi kaman ba mai kudi ba, murmushi tasakeyi tana addu’a yayi yadawo koba komi zama kusa da ita ya yanda yake mannanna mata kiss a kumatu na mugun burgeta, harta rabu da Mudi baitaba sumbatar bakinta ba bamasa cire kaya, hawa gado kawai zaiyi yaja wando kasa bayan minti daya ya sauko yana gyara mazagin wando batare dashi yaga al’auranta ba ko ita taga nashi, wai kallon wajen nakawo matsalan idanu, ita bama ta taba ganin abunba Allah sa Alhaji yana bari agan nashi ita tanaso tagani wlh, bata taba ganin na manya ba banda na kananun yaran kauyensu da akema kaciya lokacin sanyi. Wayanshi dake wajen tabi da kallo tana murmushi wai yanzu da gaske tazama matar Alhajin nan? Wannan babban wayan ya ijiye nashi kusada ita? Ohhh Allah mena maka kamin wannan babban kyautan, zanyi azumi uku na godemaka ya Allah na, sosai nake murna nazama matarshi, wlh ina zazzafan sonshi, Ya Allah ka karamai sona shima dan wlh ni ina mugun sonshi kuma kome yakeso zanmai gashi yanada kirki sosai, duk ita kadai ke tunanin nan tana shafa screen na wayan tana murmushi irin wayan mijinta din nan, jin an kira sallan asir yasa ta tashi bathroom na dakin ta shiga tana kallon kanta a babban madubin dakin wlh atampan nan yamata kyau kaman ba itaba, ga lallin yayi kyau shima, da kyar ta iya daina kallon kanta tana yaban kanta tana practicing kalan murmushin dayafima fuskanta kyau da zata dinga ma Alhaji idan yana kusada ita yana kallon fuskanta, tadauro alwala tazo tayi salla kan dadduman dake gefe guda adakin. Kusan awa daya yayi sannan yashigo gidan dawani babban akwati wuraren 5:15, dakin ya shigo bayan ya ijiye babban ledan abinci dayayi order a nan dinning, tana kwance kan gado adan takure wani dan gajeren bacci yayi awon gaba da ita ijiye akwatin yayi sannan yataho gaban gadon zama yayi abakin gadon yana bata wani close look, Ummi nada kyau fa kyau sosai and she’s so young batafi 23ba highest 24maybe, batada jiki sosai but tanada hips wanda tana samin kulawa zasu fito da kyau, ga kindirmo fam, tanada bakin gira acike da dogon gashin idanu her lips are not sooo pinkish black lips gareta with a slight pink middle ga bottom lip din is a bit chubby na saman kuma a bit thinner compare to na kasan hakan yasa lips nata looks so succulent irin savage lips din nan gareta, ga pointed nose, abinda yafi kasheshi is her black skin kodan shi fari ne oho but black skin din Ummi is art for him, he loves looking at it kodan rayuwanshi he’s surrounded with fararen mata ne oho dan iyayenshi are fair hakama kannenshi dashi gakuma family su Hadiza da ita kanta Hadizan are fair saisa black skin na Ummi is bewitching him, ahankali yakai hannunshi yadaura saman fuskanta saikuma kawai ya kwanta gefenta yasa filo abayanshi tareda jawota jikinshi adan firgice tabude idanu hada idanu sukayi ahankali yace “kwanta ajikina” yayi maganan yana sata akirjinshi cuddling her so tight kaman yanda yakema Amal, ijiyan zuciya suka sauke atare bayanta ya shafa murya kasa kasa yace “kin gaji ko”? Gyadamai kai tayi anarke ganin he’s so caring, peck ya manna mata agoshi yadago yace “sorry Ummi na, bari na dan matsa miki jiki” yayi maganan yana kai hannunshi bayanta yaja zip nata kasa dasauri ta kankameshi wani kalan kunya takeji, the way ta manna boobs nata akirjinshi dudda it wasn’t intentional jiyayi yadan birkice, hannunshi yasa yazare dankwalin kanta ya manna bakinshi kan kanta yace “kunyana kikeji bakiso nagan miki noo…….”? Dasauri Ummi na kankame akirjinshi ashagwabe tace “uhnnnnn karka fadi sunnan niiiiiiiii” yanda taja nii din kashe Nura tayi shima kaman yana wani magana da Amal yace “to bazan fadi ba toki tsaya na cire rigan kinji Baby Ummimy na” kaman zata fashemai da kuka tana dan iskan narkemai kaman ba Ummi ba murya chan kasa kaman fa wata jaririya tace “toni karufa idonka My Noor” dasauri Nura yakulle idanunshi kaman zai haukace yace “to….to na rufe kalli fuskana kigani Noor dinki yarufe” dan ciro kanta kadan tayi daga kirjinshi takalli fuskan nashi ganin yarufe idanunshi da gaske yasa taidan murmushi ciki ciki ganin shagwaban yagama siyeshi tanajin wani wutan sonshi azuciyanta, Nura yace “kinga na rufe idanun ko bari in cire to, tsaya ahaka yar karaman Babyna Ummi” wlh Ummi wani mahaukacin so takema Alhaji bata taba sanin he’s this sweet and easy going ba, itama batasan daga ina wannan son yake zuwan mata ba, ahankali tace “tom banda yar cuce” dariya Nura yayi yace “na yarda” ahankali Nura yakai hannunshi saman kafadanta dan yariga ya zage zip din yashiga sauke dogon rigan nata kasa wani irin sauke ijiyan zuciya Ummi hannunshi akan skin nata is like tafiyan matsassaku ajikin mutum is just too refreshing, slippery sweet tanajin yirrrrr ajikinta, bako musu tabarshi ya yajaye rigan boobs na fitowa, saida yakai rigan waist nata sanna yabarshi dasauri Ummi takara shigewa jikinshi ta kankameshi tana sauke ijiyan zuciya dasauri sauri kaman yanda shima yake saukewa ahankali yabude idanunshi yakalli fresh smooth bayanta babu wani tabo ko mark kodaya abayan ko pimple gawani nude bra data saka mai kyau, hannunshi har rawa yake yakai yadan dago fuskanta sama tareda daura nashi akan nata, gently yadaura bakinshi kan nata yana budewa ta tsaya cus she’s just enjoying komi, bakin Alhaji akan nata kafin yatura duka harshenshi cikin bakinta yana kissing every single place na bakinta yana juyoda ita ahankali da dabara yana maidata katifa shi yana zuwa samanta, Ummi bata taba sanin haka akeji idan ana kiss ba kasa hakuri da jurewa tayi takai taki hannunshi dasauri tana kama waist nashi gam tarike tana tsotsan tongue dinshi kadan kadan dudda she’s trying not to takasa dan wlh bakin Alhaji dadi, harshen shi kaman yagama shan minti ne yazo yama sumbatar ta ashe haka sumbatan mutum keda dadi, yanda Ummi ke sucking tongu nashi kaman she’s about to chew it or swallow it Nura yaji kaman he’s about to die sabida pleasure, ba’a taba mai this thing she’s doing ba, and tanayi with so much love da jikinta ke fadi irin mutum yaga wani sabon adventure dabai taba sanin yana existing ba, suna kiss din yana wani kara bounding souls nasu Nura yabarta tana experimenting bakinshi kaman vampire shan duk inda tasamu taje har hakorinshi saida tabi ta tsotse, Nura yaji he’s just crazy about her. Ahankali Nura ke sauko da hannunshi yana sauke hannun bra dinta daga shoulder nata kasa duka biyun kafin dawani irin sauri yadaura hannunshi saman left booby nata yawani squashing dasauri Ummi tace “assshhhhh! Wayyyooo Allah na Talatuwa” bata tabajin dadi kaman yanda taji yanzu ba daya kama mata nono yamishi matsan da akema tumatiri kaga ruwa ya feso, Hannunshi har rawa Nura yake dasauri yawani ja bra din kasa shima yakishi waist yakai hannunshi dasauri duka biyun yayi grabbing boobys din da kyau yayi squeezing dasauri cikin hargitsastsiyan murya yace “Ummimy na kinada manyan nonuwa washhhhh” yasaki bakinta dasauri yadago kanshi yakalli kirjinta dan yakasa gasgata abinda yaji yarike just now da hannunshi, birkicewa Nura yayi ganin wasu kalan sexy black boobs masu super dark areola da nippi, so big and full, gasu so firm, irin cikakken kindirmo Ummi kedashi, dawani kalan sauri Nura yay squeezing nasu assuring kanshi these are now his yana wani sakin malalacin ihu kaman wanda notic kanshi ya kwance yace “Hajiya Ummi dama haka kikeda kindirmo? Wash ni sha zanyi wayyo ya Allah” dawani irin sauri abala’in kunyace Ummi takai hannayenta tarufe tareda mirginawa tai kwanciyan rub da ciki feeling wani irin ecstatic sensation ako’ina na jikinta tanajin dadi dakuma kunyan yanda ya yabi kirjinta, she just want him to come to her, toss her, flip her and suck the hell outta them harsaiyaji yakoshi bazata taba yima Alhajinta rowa ba, ko rayuwanta yakeso zata bashi bari nono. Wani kalan tashi Nura yayi dasauri yashiga cire kayan jikinshi anan kasan daki ya yar yazo wajen gadon ahankali yasa hannunshi yakarasa zare dogon rigan daga waist nata ya yar akasa nan inda kayanshi shima suke, ass nata ya bayyana wearing wani g-string da Meena tace shi zata saka yau shima nude, is like all the ass na waje kaman ba’a saka panty ba, ahankali Nura yakai hannunshi daya yana grabbing front na boxer nashi yace “la’ilaha illallahu, never knew dark skin ass is this lush” kasa controlling kanshi yayi yakai hannunshi yabawa wajen wani naughty spank ass din yayi wani babbarrrr Nura zarewa yayi yace “what a naughty jiggling ass kikeda shi Ummi” kawai yakai fuskanshi yadaura akai ya manmmanna ma ass din kiss kafin yay cupping ass din da two hands nashi yana kallo yace “this is magnificent Ummi” kara bama ass din naughty spank yayi cikin pale voice Ummi tace “auuuuchhh!” Wani kalan badddd smile Nura yasaki jinshi yake kaman yaune rana na farko dazai fara abu da mace kaman yau yafara aure the feelings is overwhelming, ahankali yakamo kafanta yakai saitin fuskanshi sauke bakinshi yayi tareda mannawa cute feet’s nata dasukaji jan lalli kiss mai kara muah! Wani irin damp breathe Ummi tasaki. “Uhmmmmm!” Bama tasan nishin yafito ba, bakinshi Nura yabude yasaka babban yatsarta ciki kafin ma ya tsotsa Ummi tawani kalan jirkito tajuyo from position datake akife tace “wayyyyoooo waiwayi kabari Alhaji” kambu jitake kaman zata mutu jin yatsun kafanta abakin Alhaji kafanta yafara rawa trying to pull it outside yaki saki, sucking toe din yayi yana kara tura remaining toes din cikin bakinshi flicking and f*cking inbetween toes din da tongue nashi dayasa Ummi ta tashi zaune a birkice. “Na shiga uku Gwaggo wlh zanyi fitsari” kawai ta fizge kafan dan yacigaba she can peee ajikinta ayanda takeji ta taho bata damuba kaman mahaukaciya tafado kanshi daga gadon zuwa nan kasa ta saki wani tsinannen kuka kaman yar jaririya dawaniyi daburta Nura completely yace “sorry baby na, sorry sorry, Oya Oya ya isa, menene kike kuka? Nine nake neman saki kifara amalala” Tana wani mannamai erected nippis nata with style a kirjinshi kaman yaran dabasu iya magana ba tana tsinannen kukan tace “bakaine ke mini waiwayi ba akafa kanamin susan kadangare” cikin kololuwan sha’awa Nura yace “Ummi kan nonuwan nan naki chakchakana suke wlh Ummi zan zare akanki, ki bani Insha haba babyy na, zomu kwanta nasha kindirmo muyi bacci”. Ooops see yaaah Saturday😍 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR BONUS💃 EPISODE 🔟 Baijira amsanta ba daukanta Nura yayi still malalacin kukan takemai dake wargazamai electricity brain ya kwantar da ita agadon yana kwanciya a gefenta bayanta yashiga tapping yace “lub lub lub yar yarinyata daina kuka Noor dinki ne”? Gyadamai kai tayi ashagwabe, dasauri yace “to nadaina, amman nasha kadan eh Ummimy na, Insha kindirmon?” Alalace ta gyadamai kai cikin hatsabibiyar murya tace “amman dan minini zafi sukemin dukka matse kan” har wani haki Nura yake dasauri yakai hannunshi yarike kafin dasauri yadaura bakinshi kan daya jiyayi nipple din kaman kwan boris abakinshi zuka yayi dayasa Ummi tai ihuuu. “Asssshhh” taja baya kaman zata cire biyota Nura yayi dasauri sucking them hannunshi dayan yana murza kan daya the way takeda kan nipples completely killed him cus Hadiza batada kan nono haka, koda ta haifi Aman saida aka fito mata dasu a hospital, Ummi jitayi Alhaji zai kasheta bura’uba dama haka akeji kodan Mudi baitaba shamata bane, ita bama tasan takamaimen metakeyi ba but turamai boobs din tayi giving him full access tanajin dadin dabata tabaji ba wani kalan fitsari taji yacika mata mara dasauri tashiga komawa baya tana nishi Nura nabinta kaman yaro da ake kokarin rabashi da nono yanabin Maman, sake sakin kuka Ummi tayi Nura yariketa gam yaso sai bayan isha’i wani abu zai shiga tsakaninsu but yanzu manta meyakeyi yayi he just want sex badly, yadade baiji wannan epic sha’awan da pleasure ba, at a point ma manta yanada jijiya acikin wandonshi yake but yau shine he’s dying yasadu da Ummi, jiyake da zata hanashi har kuka zai iya saki sabida yanda yakejin kololuwan sha’awan nan, gajeren wandonshi yashiga ja kasa yana gurzan boobs nata abaki tass yacire yaja g-string din nata itama yacire ya yar, da karfinshi dan yasan tayi aure yana addu’a yakai wajen yabuga but bam, Ummi tadanyi kara jin zafi dan kaman bama ayi kofa awajen ba sake komawa yayi yana nishi sosai but yaki shiga adan rude yasaki boobs nata yadago kanshi yakai hannunshi yana share fuskanta yanda take kuka dasauri muryanshi baya fita sosai kaman mai whispering yace “Ummi wanda kika aura bai miki komi bane bakince kin haihuba”? Gyadamai kai tayi tana kuka ashagwabe tace “uhm na haihu but dan cikin bai nunaba” sake knacking wajen yayi yana kallon fuskanta Ummi tafashe da kuka tace “wayyoo Gwaggo zan mutu kadaina Alhaji” kasa dainawa yayi yacigaba bayan yariketa da kyau but still jin ana kiran magrib yasa yadaina ahankali tareda grabbing lips nata yashiga kissing nata da sauri while squeezing her boobs da kyau almost 6mins yayi ahaka saida tadan daina kukan sannan yasaki lips nata cikeda mugun so sama da wanda yake mata da yace “stop crying daina kuka to nadaina” gyadamai kai tayi idanunta arufe yadago yajuya yawuce bayi dasauri ummi tabude idanunta kadan tabishi da kallo he’s so big jikin Alhaji kaman jikin mutanen dasuke gani yan kasan waje a tv ga abinshi kato kuma atsaye yanzu duka wannan zai samata ai zata mutu, yanzu da gaske Baban su Amaly yake gani haka ba kaya shima ya ganta ahaka sun zama daya wlh she’s so happy tana mugun son Alhaji sosai sosai. Fitowa yayi daga bayin yazo gadin daukanta yayi yace “muje muyi wanka” manna fuskanta tayi akirjinshi yanabin jikinta da kallo kaman maye, shi dariya ma tabashi har suka gama wankan taji bude idanu jin an tasa salla dasauri yafito yabarota abayi agurguje yasaka jallabiya ya feffesa turare tafito tana tafiya ahankali tana mamakin zafin dataji dazu bayan ta taba aure kuma ai Mudi yana mata kusan duk sati sau biyu wani zubin uku ma but maisa taji zafi? Hijabin datagani a wardrobe taciro dawani shegen half gown na bacci cream color silk material dakeda wani transparent light laces pattern tasaka yama jikinta kyau tazura Hijabi tai salla tai addu’a sosai a sujjada. “Ya Allah ka albarkaci aurena da Alhaji in kasance matarshi har a aljanna, Ya Allah wlh ina sonshi sosai Allah kasa yasoni fin yanda nake sonshi, Ya Allah kabani ikon farantamai rai kabani babban matsayi aranshi, wlh inason Alhaji, ina mugun sonshi” dudda haka tagama addu’an Allah Allah take yadawo kaman tabishi masallacin tadauko shi ita bazama ta iya bayanin yanda takejinshi aranta ba gashi abubuwan daya mata dazu Mudi bai taba mataba kaman karya dena shamata nono wlh, da yana sumbatarta lokacin har wani shaukin sonshi da begenshi ke kara shiga ranta, murmushi tayi ta keanta kan dadduman tana tuna duka abubuwan daya mata just now da yanda taga dukta rudashi da tanamai shagwaba aiko zata dingamai tashi tayi tana tunanin ina wayanta yake Dan Meena ta hadamata abubuwan ta toko yana akwati ta da akasa a mota wannan akwatin ba shine nataba kuma taso taduba group na Matan Auren M shakur taga me M shakur tayi takara koya bakaramin jin dadin class din tayiba ganin da hausa akeyi dan batawani gane turenci sosai, ahaka ma wai next week M shakur zata mata private class da Meena tabiya mata that means zata gama da Nura gabaki daya, M shakur bayanin komi dalla dalla take da gif images danka gani ka gane ka koya, tanason malaman wlh tayi ne. Murmushi tayi tai juya ahankali tace “wlh bakin Alhaji dadi ga gardi, kawani kalan kamshi ga dan gishiri gishiri yawunsa abin gwanin dadi kaman wanda yasha farin bitamin c, laaaa banyi brush ba banso yaji kowani kalan wari ajikina ko bakina” tashi tayi dasauri tawuce bayin gako brush sababbi guda biyu daukan daya tayi tabude tai brush tadauki mouthwash datagani awajen tasanshi ta kukure baki ita kadai fa ta tsaya agaban madubin bayin tana gwada kalan shagwaban dazata dingamai. “Inyaaaaaa Alhaji zafi kasana kemini” dasauri tana kallon madubin tace “a’a harda yarfe hannu zan dingayi inadan hawaye in kashe murya” ta gyara tsayuwa tana kashe murya tace “My Noooorrrr baapi kasana aaaassshhhh, ni oh’oh kada ka kara” wani kalan murmushi tayi tana rufe fuskanta tace “wlh wannan zanyi yafiyin kyau koni na burge kaina” murmushi tasakeyi jin ana kiran isha’i yasa tasake tara ruwan zafi tayi tsarki da kyau tana kara wanke ko’ina na wajen bata saka pant ba daman tadauro alwala tafito takosa yadawo salla tayi sannan takara komawa gaban wardrobe tabude neman turare take kaman ance ta taba wani drawer taga turaruka daban daban na mata aiko ta feffesa tadauki man baki ta shafa abaki tamaida komi tadawo kan gado tazauna, tana nan zaune yayi sallama tareda bude kofa wani kalan farin ciki da murna daya kama Ummi, wlh ko kadan batasan sanda ta tashi da gudu tazo wajenshi tawani fada jikinshi ba ta kankameshi tana murmushi sosai tace “sannu da dawowa” abin wani kalan dadi yama Nura cus the hug was from her heart it shows presence nashi means a lot to haka, manna mata peck yayi akai yace “oyoyoo Hajiya Ummin’s kinyi kewana?” Gyadamai kai tayi tana murmushi yace “kinyi salla?” Sake gyadamai ki tayi yace “kinada alwala?” Sake gyadamai kai tayi yace “dauko Hijabi muyi salla” sakinshi tayi akunyace tajuya zai bita da kallo yadaure yahana kanshi sabida alwala salla yajasu bayan sun idar yakama kanta yayi addu’a sannan yamike tsaye yana dagata da kanshi ya linke dadduman sai kawai yaduko agabanta yace “hau babu muje kasa muci abinci” wani kalan murmushi tayi dasauri tahau tunda yamadata Amal yau, yace “good gurl” yana goyeda ita suka shiga saukowa har dinning abincin daya ijiye dazu Ya kwasa batare daya sauketa ba yawuce kitchen da ita yace “bari namana microwaving” dasauri Ummi tasauko daga bayanshi tace “kawo nizanyi” taja kujera tace “Kaika zauna” wani kalan kallo yamata dasauri tadaura hannunta daya a fuska tasa dayan hannun ta karba ledan tawuce shikuma yazauna kan kujeran yana binta da kallo yana appreciating what she just did, gaban microwave taje tasaka ta kunna tayi aiki agidajen Abuja she can use all this things. Batare data juyo ta kalleshi ba tace “akwai kayan shayi agidan namaka”? Ahankali yanabin dogayen cinyoyinta da kallo zuwa ass nata yace “na manta ban siyoba” gyadamai kai tayi tacigaba da tsayuwa awajen awani kalan hankali authoritatively yace “zonan Ummi” dasauri tajuyo takalleshi hada ido sukayi cinyanshi ya nunamata hakan yasa ta taho ahankali ta tsaya gabanshi hannunta yajawo ya daurata akan cinyanshi ahankali yakai fuskanshi wuyanta yana shakan kamshin datakeyi murya chan kasa yace “kina kamshi mai dadi my baby” kiss yasakin mata awuyan dasauri ya lumshe idanu nipples nata shooting out Nura yabisu da kallo hakan yasa yacigaba da manna mata kiss tanan saman rigan baccin yadaura bakinshi yakama rigan da nipple din yadan ciza kadan, ihu kadan Ummi tayi. “Wayyoo Dadyn Amal cizo, abincin yayi zafi” batare daya saki nipples dinba yace “nima nayi zafi” yasake cizan ta dayasa Ummi tayi nishi tana turamai kirjin hannunshi yasa a dayan yayi squeezing tareda jawoshi ta rigan kaman zai katsa dasauri Ummi tace “na shiga uku zai katse fa” dan murmushi yayi ya mike tsaye yana dauke da ita dasauri tarikemai kanshi fridge yaje yasa hannunshi yaciro yoghurt yabude yakai bakinshi yasha sosai sannan yacire yakai bakinta yace “sha” batai nusu ba tasha tacire kai tace “ya isheni” maida yoghurt din bakinshi yayi yakarasa sha sannan ya ijiye goran yafito daga kitchen din yana kashe wuta dasauri Ummi tace “abincin fa” idanunshi sundan kankance yace “ke zanci amadadin abincin tunda kin tayarmini da sha’awa” dasauri taboye kanta awuyanshi ahankali tace “dan Allah kaci abinci banso ka kwana da yunwa” kashe wutan falon yayi yana hawa staircase da ita yace “tonight of all nights bazan taba kwana da yunwa ba, trust me full platter na earth food yau zanci bama na sea food ba” kashe wutan saman yayi yawuce dakinshi da ita maida kofan yayi yarufe yashigo dakin gaban dressing mirror yaje yaja kujeran wajen ya duka yasauke Ummi akai taredakai bakinshi saitin kunnenta yace “bude idanunki and kada ki kara rufewa” gyadamai kai tayi tareda bude idanunta ahankali ta kalleshi yana tsaye agabanta idanunshi sunyi jaaa sun kankance looking very wild kaman ba Alhaji ba, kanshi ya nuna yace “keep looking at me” gyadamai ki Ummi tayi dan tagane turencin, ahankali yakai hannunshi wuyan jallabiyan shi yacire boturan tareda kwabe jallabiyan dasauri Ummi tai yunkurin rufe idanu Nura yace “nace kada ki kulle ki kallen” ijiyan zuciya tasauke ta kalleshi Alhaji fari ne sol yanada broad chest dakeda gashi a kwance yanada dan teba kadan but ba irin manyan nan ba kaman randa at dsame time ba flat tummy gareshi ba but jikinshi nada kyau ga boxer shi yawani mike gaban, Nura na kallonta kaman yanda take kallonshi idanunshi sunyi jazur yaki hannunshi yana shafa tundaga wuyanshi yanakai hannunshi down yana kallonta Ummi jitayi kaman tanajin fitsari dasauri ta hade kafafunta tana kara sauke ijiyan zuciya ahankali yakai hannun nashi saman maranshi dakeda gashi kadan kafin gently yayi sliding hannunshi cikin boxer nashi. “Hmmmmm” Ummi tasaki wani wawan ijiyan zuciya kaman magic, ahankali Nura yaciro erected joystick nashi da head din was dripping wet cikin yar kankanuwan murya yace “kinga abinda kikamin, zaki sha?” Da sauri Ummi ta gyadamai kai tana kallon abin bata taba ganiba sai yau and is big fari sol dashi, avarage ga big red crowns, takowa Nura yayi zuwa dab da ita her eyes na kara kasheshi sabida yanda yake ganin how much she wants abin da yanda take kallon abin, yanada wani dabi’a na son yaga matanshi wants him yaga she really do, abinda baitaba gani for once awajen Hadiza kenan ba, ahankali ya goga abin a fuskan Ummi slapping her dashi gently cikin muryan wanda kinsan baya cikin hayyacin shi yace “girmanta tamiki ko tamiki karama?” Rawa lips din Ummi sukayi jin yanda abin yataba fuskanta yana goga mata some little juice a face dakeda sanyi tace “bantaba gani ba sai yau” yana wani kalan kallonta yace “to gata yau kin gani tun yanzu kimata kome kikeso kimata dan yau zata gwada miki batada mutunci, kinaso ki sha kiji yayake”? Dasauri Ummi ta gyadamai kai tace “eh in sha?” Kai matashi kan lips nata yayi yace “tsotseta kaman nabaki alawan dayafi duka alawan duniya dadi” bude bakinta Ummi tayi da sauri Nura yawani lumamata abaki wani kalan juya idanu da Ummi tayi zaka dauka Aljanu sun bugetane tace “uhnnnnnnnn uhm, huuuuuuiiii” ihu Nura yabuga “aaaaaghhhh Ummi, Baby na la’ilaha illallah Ummi kin iya sha, Ummy kin iya sha, waiii ahhhhh!” Yayi maganan yana ciro joystick din dagudu daga bakin Ummi ganin tana neman tasa yakawo baisan kodon ba’a saba shamai bane fizgota yayi yadagota yasata ajikinshi yakama bakinshi yafara kissing nata kaman jira Ummi take itama tashiga kissing nashi yanda sukeyi kaman 2 hungry people yana juye juye da ita adakin ya matseta sosai ajikinshi hannunshi daya na spanking ass nata daya na squeezing booby, Ummi jitayi kaman zata mutu da dadi yasa itama takai hannunta daya saman nonon shi ta murza kan saida Nura yawani bankaremata yazabura kaman wani fizgagge anan tsaye yakama dayan hannunta da sauri yakai kan joystick nashi kamawa Ummi tayi tana wasa dashi shikuma yakai duka hands nashi yana bawa boobs nata handwork suna tafiya kadan kadan suna nishi har sukakai gado suka fada yanda Ummi ke sucking tongue nashi da lips u will think zata cinye bakinne batare data ragema Hadiza anything ba, a daburce Nura yasaki bakinta yana dagota zaune yacire rigan baccin ya yar yana daurata akanshi ya kwanta yakai kanta wajen joystick din while her face sitting akanshi kawai Ummi taji bakinshi right there, ihuuuuu ta kurma ta mirgina zatai tumbling tafada akasa da kyar Nura ya rikota jikinta was vibrating ya riketa ajikinshi gamgam cikin muryan dabaya fita kaman mai whispering baimasan meyake fadi ba yace “bantaba shan gaban mace ba ki barni nasha naki Ummi, shiiiiii zakiji dadi bari na shanye ruwan kinji” bamata gane komi tadaiji ya kwantar da ita she don’t even know what was going on kawai taji bakin Alhaji awajen yana drinking she completely and totally lost it dan Batasan something like that na duniyan nan ba da duka muryanta tace “Mamaaaaa ga wani yana shan gabana, Alhaji wlh da dadi na rantse zan mutu, tafarfashashen dadi abin nan yake mini, Alhaji kaji tausayina, wallahi wallahi nace maka tafarfashashen dadi yake mini, Innalillahi wa innailaihi raji’una Alhaji yasin yasin zan saki fitsari, wayyooo Allahna, wayyo dakalin, damdamalin, kwanan, kwarin dadin rayuwata, Alhaji kana tsotso mini rayuwan dadi na, Alhaji kana shayar dani mashashurin, tsubaragen, tsantsagwaryan, rusheshen dadi, Talatuwaaaaaaa!” Ummi tai ihuuuu jikinta ko’ina kaman an jonata da electric current, kaman taje septic shock Nura has never ever felt this pleasure dayajeji ganin yanda yafitar da Ummi daga right state of mind dinta, haka yakeso yama mace abu ta nuna taji dadi ta manta tarbiyan gidansu ba irinsu Hadiza dabama sa reacting ba kaman kaine ke kidinka kake rawanka, tasowa yayi yakamata yasata ajikinshi yana karanto addu’a kafin yakai bakinshi kan nata yafara kissing nata dasauri Ummi takama bakinshi kaman her whole life depend on trying to get herself back, put her self together, mercilessly Nura yafara shiganta. Ladies come close, listen this erotic scene bawai ina yinshi for fun bane, NO! I want you kugani ku karanta and ku koya, learn to return favor when u and ur man gets smooching. Kunsan akwai Matan da Maza zasuce ma oya bend doggy zamuyi today suce no su bazasuyi ba adaiyi na kwance e.g Hadiza Wani yace shamin mata tace no bazatayi ba, batason shan kayan aiki. Wani yace haukai ki tukani yau tace no bazata hauba idan shi bazai mataba abarshi. Idan ma aka fara some mata feels like nunama miji kinajin dadi, the prick dey sweet u abin kunya ne. Please why??? I say why??? Join my matan aure class dazanyi next month and learn registration is just 2k please kudaina all those kind abubuwa yanasa maza to loose interest in you. This book MATAN KO MAZAN is for all of us, life lessons, abubuwan dake kawo major matsalan aure nake discussing, while u enjoy reading make sure kina picking one or two things as darasi. M shakur✍🏻 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣1️⃣ #Ad Akwai wani cuta da ake kira da POLYCYSTIC OVARIAN SYNDROME(PCOS) wanda ake samun shi a mafi akasarin mata. -CUTACE DAKE HAIFAR DA RASHIN HAIHUWA A KASHI 70-80% NA MATAN DAKE DAUKE DASHI. -CUTACE DAKE HADDASA RIKICEWAR AL’ADA -FITOWAN GASHI A GEMU,SAMAN CIKI,KIRJI DA BAYA -TUMBI -KIBA -KURAJE A FUSKA -YAWAN KWADAYI -YAWAN KASALA -RASHIN SAMUN BACCI DA DAI SAURANSU . -SHIN an tabbatar miki da cewa kinada wannan cuta da akema lakabi da PCOS kuma kin rasa yadda zakiyi? -SHIN kinyi amfani da duk wani mataki da kikasani amma kin kasa cin karfin CUTAN? SHIN kinata kokari kisamu JUNA BIYU amma har yanzu shiru ba labari? Toh sha kuruminki,nesa tazo kusa,dan 4WEEKS REVERSE PCOS SYMPTOMS CHALLENGE DINMU zai taimaka miki wurin samun cikan burinki. KUMA ABUN ALBISHIR SHINE,ZAKI IYA SHIGA CHALLENGE DIN A PROMO PRICE NA NAIRA 5000 KACAL. Abunda kawai kike bukata shine JAJIRCEWA da kuma NACEWA. Zaki iya shiga kungiyar mata masu wannan CUTAN a WhatsApp ta wannan link din https://chat.whatsapp.com/I15myu04O5i8f8DAyTxi1d DOMIN SAMUN INGANTATTUN BAYANAI GAMEDA WANNAN CUTAN ⬇️ https://chat.whatsapp.com/I15myu04O5i8f8DAyTxi1d. Ko kuma kiyi subscribing YouTube Channel dinmu ME SUNA LAFIYAR MATA TV domin samun video duk sati akan wannan cutan ta wannan link din ⬇️ https://youtube.com/@LafiyarMataTv?si=mugBUh7hcuWFvezV Episode 11 Wuraren 4 na asuba wayan Nura yashiga ruri da kyar ya iya yabude idanunshi dan rabonshi dayayi bacci irin mai dadin nan harya manta, hannunshi daya yazare ahankali daga saman ass din Ummi dake bacci ajikinshi sun rufa da bargo yadauko wayan ya kallo screen din ganin Wife yasa yadan danna gefe sabida wayan yadaina ringing ya ijiye, wayan na katsewa wayan yashiga ringing again agajiye yakai hannunshi yadauki wayan tareda picking yakai wayan kunnenshi kafinma yayi magana Hadiza kai tsaye tace “kana ina Nuri? I know ka kwashi yarana baka sanar da ni inda ka kasisu ba but at least nasan kai kana kwana agidan ina kake yau baka kwana gidan nan ba, kana ina Nuri”? Hadiza tamai ihu kaman tana magana da wanda ta haifa, wlh yamanta menene bacin rai arayuwanshi daga jin muryanta har ranshi yasoma baci da asuban farin nan just imagine, daurewa yayi batare daya daga muryanshi ba gudun kada yatada Ummi yace “ina inda nakeda farin ciki da kwanciyan hankali I can’t stand gidan dakika maida bola da abincin dasuka baci a ko’ina” sosai Hadiza taji ranta na tafarfasa tace “kadaisan ni ba kazamiya bace kuma nafi karfin ka kirani kazamiya wlh, yar aiki kuma ana kan nemo mini wata and ba maganan dana kira nayi dakaiba kenan, kana ina? A ina ka kwana eh Nuri? Where are you?” Batare daya daga murya ba yace “baki da hadi da inda nake” yana maganan ya katse wayan daga kunnenshi wani kalan ihu Hadiza tayi tana karabin dakinshi da kallo dataga an chanza komi na dakin hadda penti da furnitures kasa daurewa tayi ta dannamai kira ahankali Nura ya jaye Ummi daga jikinshi yasauka daga gadon yadauki wayan yafita daga dakin yana sauka kasa yadauki wayan ganin bazata daina kiraba tace “Nuri where are you?” Dan tsaki Nura yayi yace “me ruwanki da inda nake? When did you starting caring about inda nake?” Cikin fada tace “I’ve always cared, ya za’ayi mijina bai kwana agida ba kuma bawai cemin kayi zakai tafiya wani wuri ba bazan tambayeka ba, kana ina Nuri? And yanzun nan nashiga dakinka naga ansa new furnitures an ciro komi nada maisa bakasa an chanza funiture gidan gabaki dayaba saina dakinka kadai”? Akufule yace “banga dama ba” dan shiru Hadiza tayi saikawai taji gabanta na fadi tace “Nuri a ina ka kwana?” “Bakida right din sani” wani abu Hadiza taji ya tsayamata awuya abubuwa dayawa na zuwan mata rai, zata sake magana Nura yazare wayan daga kunnenshi ya katse tareda kashe wayan ma gabaki daya cus amarcinshi yakeso yayi in peace barin wayan yayi anan ya hayo sama cikin bacci Ummi taji ana lalubanta dudda ta gaji hakanan ta hakura yanda Nura keyi kaman yanzun ne yafara saduwa da mace bakaramin dadin Ummi yajiba dan batada wani maraba da virgin ga dumi kaman oven. ** Kaman bazata daga wayanta ba saikuma ta daga tace “Ya akayi Hadiza”? Dan shiru Hadiza tayi saikuma chan tace “Anty Jams kinga ko akwai wani kalan silent bakin and cool mugunta da Nuri ya iyamin dake cimini zuciya, yake kuma bakantamini rai” yanayin yanda Anty Jamila taji muryanta yasa tace “yanzu kuma meya faru?” Cikeda damuwa sosai kaman Hadiza zata fashe da kuka tace “tun bayan sakin nan Nuri ya chanza gabaki daya, wlh bana gabanshi at all baya kulani, yau 5days kenan daya kwashe su Amal da Aman I have no idea inda yakaisu, ranan yadawo ya kwana agida to tun ranan bai kara kwana agida ba yau 4days kenan baya kwana agida, kuma bai sanar dani zaiyi tafiya ko zaije wani wajeba, ranan danai noticing bai kwana gidaba I called him da asuba ina tambayanshi yana ina ke kinji yanda yake amsani ne kaman ba Nuri na ba, yana gayamin banda right na in sani daganan ma kashe wayan yayi Anty Jams har yau nakira wayanshi akashe, wani zubin kona kira naji call waiting yana gama wayan dazaiyi saiya kashe, i WhatsApp him, namai dropping imessage, namai sako a IG duka babu wanda bai duba ba yaki kulani, bakiji yanda kirjina kemin daci ba wlh jikina nabani wani abu ina yake? Ina yaje yana kwana? Yana ina?” Duk sauraron ta Anty Jamila tagama tace “meya jawo ya barmiki gidan?” Danshiru Hadiza tayi tace “nasan ina gayamiki zakihau mini masifa but please understand me Anty Jams this is Abuja city of wealth, this is how we roll, Anty Jams kinsan menene yar aikina Ummi nan tayi tafiya zuwa kauyensu an kirata wai kanka ta ba lafiya bla bla bla shine ta tafi, ranan dana dawo kaman yaran nan zasu kasheni da aiki haka na dafa mana indomie Anty Jams wlh ni nama manta yanda ake girki yanzu I can’t even stand heat din kitchen ai sai fatana ya kode bayan uban kudin danake zubawa a skin care dina” “sannu diyar qaruna, idan akaji kina magana wani zai dauka Obasanjo ne ya haifeki ko Bill Gates, Hadiza nasan ni yayar ki ce i oath to support you but listen wlh wlh bazan iya supporting wannan rayuwan dakikeyi ba ayanzu, Hadiza this is not you ba tarbiyan nan Mama tabamu ba, ni kafin kigama bani labarin nama gane karshen nasan kinki yin komine ya kwashi yaranshi yakai inda za’a kula dasu, Hadiza you’ve failed as a wife already, yanzu kuma you are failing as a mother ace yaranki just su biyu bazaki iya kula dasu ba Nura ya kwashesu yatafi dasu wani waje” rai abace Hadiza dake fama da bakin cikin Nura tace “Anty Jams I think this is the last time zan kara kiranki nagaya miki damuwata for crying out loud when will u drop all this sentiments da mentality kusayawa yan kano and just look at me like an educated smart lady data zagaye kasashen waje? Eh fisabilillahi fa, kinzo abujan nan infact kinada friends ma acikinta, kinga yanda muke rayuwa maisa bazaki fahimce ni ba Anty jams? Menakeyi that is wrong eh menakeyi? Ba’a taba kwana agidana babu abinci ba inada mai dafawa, yarana basu taba kwana basu sami wankan safe da dare ba before bed, kome sukeso dafa musu ake, sau nawa ina cire kudi nai order expensive kids wears bama da kudin Nuri ba na sayoma yarana kaya? Bawai ina cewa Nuri baya saya musu kaya bane zai daukeshi da kanshi yakaisu different kids stores kome sukeso ya saya musu but ni kwaso musu uban kaya nake na kyalekyale different things sai kinje wardobe nasu zaki gani, headbands, ribbons menene menene I know how much nake kashema yarana, Aman nada every single collection na kids shoe da gucci suka fitar this year, Little Amal nada birkin ga receipt na handbag din worth millions duk da kudina na saya musu da zinarai, dan kunnen diamond stud ne yanzu haka a kunnen Amal ninai order shi, menene ban musu? I buy heaven and earth for them duk yar aikin dazan dauko da basaso koranta nake straight cus I wanna make my kids comfortable sune life dina, I gave them the best yar aiki dasukai approving, sukeso kuma Ummi can Babansu do that for them?? Nuri baida time na kallon yan aiki na ma balle yasan wanne yaranshi sukafi so I did all that on my own to akanme zakice I failed as a mother ko as a wife? Anty Jams Nuri yataba gayamiki yadawo daga office babu abinci agidan nan? Ba abinci about kala biyu akan dinning cikin warmers?? Ko yadawo yaga dakinshi ko bayinshi da datti ko singlets da boxers nashi ba’a wanke ba? Bazaki taba shigowa gidana ki ga datti ko daya ba akasa ko ki taka kasa, ko issues damuka samu this time kan Mamanshi sabida rainin dayamin ne sai bayan yace suzo zai sanar dani amman tunda mukai aure nataba samin matsala da uwarsa? No, mukaje kano mu sauka agidan nadan wuni daganan na gudo gidanmu so menayi? Police dana dauko is because Shegiyar kanwarsu had the audacity tashigo har gidana ta nemeni da fada tana zagina takuma yakusheni da kumbunan vampires nata, I need to show them no one can bully Hadiza in her house, so Anty Jams menene kike fadamin? Inada damuwa which kinsan bazan iya fadama friends dinaba sumin dariya bayan cika bakin danagama yi na inada karfi da iko agida suga abinda mijina kemin, I called u cus kene sister na and look at wat u are telling me eh, nayi deserving abinda Nuri kemini? Ya dannamini saki daya yanzu kuma ya maidani thrash ya kwashe yarana, shima yabar gidan yabarni ni kadai inata kwana agidan nan kaman mayya, sannan ina kiranshi yana kashe waya kuma nasan yana kunna wayanshi dan nasan dole yakira mamanshi kuma yaga messeges dina yayi ignoring, ina gayamiki kina mini masifa that i failed as a mom and a wife what have I done? Menayi? Eh”? Duk yanda taso ta daure ta rike zuciyanta kartai kuka takasa sai kawai tafashe da kuka awayan ita karan kanta bazata iya misilta kalan zafin datakeji ba na yanda Nuri ke soyata a pan dinan, ance dama blood is thicker that water wani iri Anty Jamila taji hakan yasa cikeda lallashi tace “Hadiza kinfi kowa sanin yanda nake sonki, tun kina yar karama you’ve always being my DiDi, Hadiza mun taso cikin tarbiya mai kyau muke aikin gida I remember lokacin idan yau nine da shara to kene da wanke wanke, the next day nine da wanke wanke kene da shara same goes for girki, Hadiza Baba da Mama nada rufin asiri mun taso bamu rasa komiba but we were trained muma kanmu komi muke wanki, muje aike bamu da yar aiki Hadiza, mun taso munga yanda Mama kema Baban mu girki tabashi, tamishi komi, Nura ya nuna shi girkin ki yakeso yaci how many minutes zai daukeki kimai? Is just breakfast and dinner da rana yana office, Hadiza Nura ba dan Abuja bane that’s wat nakeso ki gane bazamfare ne girman kano, ya nunamiki he doesn’t want the Abuja lifestyle dole ne saikinyi lifestyle din to please your friends and co? This is peer pressure Hadiza, must u do abinda kikaga anayi agarinku? Anyi magana kice feminism you know your rights Nura yafiki sanin rights naki tunda har mutumin nan zai bude miki kasuwanci ya daukeki kuje garuruwa ki samo contact na suppliers ki saro kaya, Hadiza Nura na mugun sonki how many men zasu iya ma matansu abinda Nura yamiki yet baki da wanda zaki cima mutunci sai shi sabida kinganshi shiru shiru baida hayaniya kuma yana sonki saikikai abusing simplicity nashi” hawaye Hadiza ta share cikin muryan kuka tace “Anty idan baka rikema maza wuta ba cin ubanka suke, ga Baraka nan mijinta juyata yake kaman lagwani, yahanata business kudi sai wanda yaga dama zai dan yammata, gashi da mata ihu agaban kowa haka kikeso Nura yamaidani? Ya takani duk sanda yaso? Noo bazan yarda ba wlh, fire for fire yanzu shine new system na zaman lafiya tsakanin mata da miji agidan aure” Anty Jamila tace “Noo fire for fire is never option, look at you yanzu jibi yanda kike kuka kina bala’in son mijinki but girman kai da al’adan yahudu da nasara yasa you are gradually loosing him” dasauri Hadiza tace “I reject it Anty Jams, bazan taba loosing Nuri na ba, yana bala’in sona, duk yan uwanshi ne da Mamanshi suka gama zugashi, Nuri baitabamin hakaba, Nuri kome zanmai baya fushi dani, baida riko ko ijiye mutum azuciya, he will still come back to me and talk to me and call me, Nuri na baitaba shareni ba, wlh all this aikin Maman shi ne da kanwarsa kuma muzuba da ni da su” girgiza kai Anty Jamila tayi zatai magana Hadiza ta tareta tace “karki damu you’ve said enough Anty Jams ko’ina Nuri yaje zaizo har nan har gidan nan yasameni bawai ina kukane sabida abin yawani dameni ba, kukan danakeyi na bakin ciki ne cus nine yakamata na dinga cusama namiji kalan bakincikin nan ba namiji ya dinga cusamin ba ninefa Anty Jams is still me Hadiza bakatakani bama nabaka hot-hot balle kuma katakani, wlh Nuri zai gane ni yagasama aya a heart, saida safe” bama ta jira amsan Anty jams ba ta katse wayan ta ijiye wayan tanabin dakinta da kallo gidan gabaki daya bayamata dadi sabida yanda ba kowa ciki, mutum rahama ne hayaniyan yaranta is something, kawai she’s not enjoying komi, mamaki take take kuma karayi itane Nuri bazai returning call nataba, lallai Nuri don get liver, tasaba saidai ita ta katsemai waya amman wai itane ya katsema waya tun ranan yaki kiranta back, yaki replying messege nata, hmmm takasa yarda ita Nuri zaima haka cus baitaba mata iskancin maza haka ba tunda sukai aure sai yau, da wannan abin har gwara ya mareta ma eh tasan mari ne bakaramin shiganta wannan silent da ignoring attitude din da Nura yamata ke damun zuciyanta ba. **** Bayan 2weeks Cur Nura yabuga two weeks yana gogan lafiyayyen amarci shida Ummi, yaki kiran Hadiza ko returning calls nata but yana kiran mai gadinshi everyweek yaturamai kudi ayi cefene wanda dama haka yakeyi dudda yasan ba girkawa zatayiba Mamanshi da yaranshi kusan kullum sai sunyi waya daman. Lafiyayyen soyayya yake bugawa shida Ummi jinshi yake kaman wani sarki ko shugaban kasa ne ma zai fadi, baitaba sanin yar kauye can give him this much respect, affection, peace and love ba saida ya aureta, wlh ayanda Ummi kemai da ace an halasta a addini cewa mata ta bautama mijinta da Ummi zata bautamai ba tantama that girl is just an Angel, saisa shima he became like a fool kome takeso koda batace tanamaso ba zai mata. Yau zasu koma Abuja jirginsu is by 1, yadan fita haka yabarta tana yima su Amal wasu kayan zaki a kitchen, dudda she’s hiding it but he could see fear a idanunta. Tana zaune a kitchen tana kallon wasu cute robobi data jera su Iloka, kwakumeti, tuwon madara, tsami gaye, gullisuwa data musu tayi shiru tana tunani, bini bini gabanta na fadi batasan yaya zata kalli Anty ba, ita tunanin ta kenan danta dauka Nura ya sanar da Hadiza, baitaba mata maganan Hadiza ba ko yace any bad thing about her kullum abunsu suke baya kawo sunan matarshi aciki. Tana zaune taji an manna mata kiss dasauri ta dago kanta Nura ne, robobin ya kwasa dagakan kujeran yazauna yana facing nata yace “ya akayi Hajiya Ummi tunanin me kike”? Murmushi tamai cikeda wayincewa tace “bakomi kawo naje nayi parking a akwati” tai maganan tana mikewa dasauri tajuyar da kanta zata tafi karaf Nura ya kamo hannunta tsayawa tayi batare daya juyoba robobin ya kalla yace “baki amsaba zaki tafi kuma gashi” dasauri takai hannunta tashare hawayen daya zubomata sannan tajuyo Nura yabi kwayan idanunta da kallo hannu tamikamai ahankali tace “kawo” kin bata yayi ya ijiye robobin a gefe ya mike yakai hannunshi kan fuskanta yace “menene? Meke damunki? Talk to me menene damuwanki Ummi”? Girgizamai kai tayi dasauri tana kokarin kauda kanta tanaso ta ture hannunshi saikuma kuka ya kufce mata dasauri ta fizge kanta ta juya tareda kifa kanta a bangon kitchen din yanda yara keyi tafashe da kuka sosai tace “ni banso nakoma Abuja kabarni anan naci amanar Anty bazan iya kallonta ba, nasan tunda ka sanar da ita zancen Auren nan zuciyanta bazai mata dadi ba babu wacce keson kishiya barinma yar aikin ka, wlh wlh Allah ma yaga zuciyana bantaba so na aurema Anty Miji ba Auren kaman amafarki haka nima naga yafaru, banda kirki My Noor, ban kyautama Anty ba” Nura yadade yana kallonta all he sees is tsantsan childishness da rashin wayau, tahowa yayi ahankali wajen yajuyo da ita hannunshi yakai kan fuskanta yana sharemata yace “jibi yanda kika bata kwalliyan dakikamin eh” ahankali tace “kayakuri” murmushi yayi this is one reason dayasa yake kara sonta she apologize to him ko bataimai laifi ba, ahankali tana jikinshi yace “bazan taba iya barin matata awani gari ba ni ina wani gari, maza dayawa na haka but ni baya cikin tsarina Inason duk inda nake iyalina na wajen kinajina” gyadamai kai tayi ahankali, anatse yace “bakici amanan Hadiza ba ni mijin mata hudu ne, nan gaba still idan naji inada bukatan kara aure still zanyi Ummi, so bakiyi laifiba” yayi maganan kai tsaye yace “dake da Hadiza dukanku matayena ne daya kuke awajena babu wacce tafi wata and dukanku kuna karkashina ne, nina aureki bake kika aure ni ba, inma laifine aure kinga kenan nine nai laaifin bakeba dan nine na aureki, idan mun koma gida ki bata girmanta amatsayinta na wacce ta girmeki sannan mahaifiyar su Aman da Amal ban yarda ki mata rashin kunya or anything ba dudda nasan ba halinki bane kada ki shiga harkanta kome zatace idan kinga bazaki iyaba ki shiga daki ki kulle kofa ki kirani muyi waya idan bananan but kada kiyi fada da ita okay” gyadamai kai tayi, ahankali ya manna mata kiss a goshi yace “Ummi ina sonki sabida kina bani kwanciyan hankali kada ki chanza daga hakan okay” gyadamai kai tayi, idanunta dasuka cika da hawaye ya kalla yanda fuskanta ya kwabe sai kawai yaji sha’awanta yakamashi hannunshi yadaga yakalli Rolex dake daure a writs nashi yace “akwai sauran time zoki bani hakkina daman jiya da daddare sau biyu kawai nayi kikahau bacci raguwa” murmushi tayi tana turamai baki kaman yar yarinya cikeda so tace “nan fa kitchen ne” yana daga riganta sama yace “eh nima ilokan wajen zan dafa a kitchen inci tunda ni bancin na roba ba” dariya Ummi tayi tace “saina cinye bakinka yau” kawomata bakin yayi yace “ai nace nabaki tunda ke kinfi son kiss kan komi kin sa lips dina sun kara pink tsabagen tsotsa oya sumbaceni” kaman jira take dasauri tayi grabbing lips nashi tashiga kissing nashi ya mannata abango yana kissing nata back yana warware wando yana ja kasa…… Saura kadan suyi missing flight nasu amman Alhamdulillah sunkai on time daman business class yabiya nan da nan sukai boarding, ashe ranan nan data daure sabida mutane ne yau harsuka sauka Abuja tana rungume ajikinshi sunyi kyau daga ita harshi ruwan amarci yasa Nura yakara haske yana sheki yadan kara kiba sabida abincin dayake samu akai akai itakuma Ummi kaman ba itaba fatanta ya goge tana sheki hannunta rikeda Samsung Z-flip dan kaita shago yayi yace ta zaba shita zaba wai sabida yanda yake budewa yana rufewa ya saya mata shikuma yana rike da hannunta suka fito suka shiga jeep dake jiransu wanda yaron Nura ne na office ya gaida Ummi akunyace ya amsa dudda tana shakkan zuwa su gida amman daurewa tayi ga mamakinta wani gida daban sukaje Nura yace “muje Muga Hajiya ko sai mu dauko yaran mu anjima saimu tafi gida” gyadamai kai tayi parking sukayi gidane babba mai kyau suka shiga suna sallama a babban falon inda su Aman da Amal ke wasa da guje guja dawata karaman yarinya dasu Hajiya da Meena da Matar Baffan shi yaran suka juyo wani irin ihu da Amal da Aman sukayi suka taho dagudu bude hannu Nura dake gabansu yayi suka taho aguje ga mamakinshi wucewa sukayi suka rungume Ummi Amal sai kawai tafashe da kuka shima Aman haka Ummi kawai ta yarda handbag da wayanta ta rungume yaran itama saiga hawaye shiru daga Nura har duka yan dakin sukayi suna kallonsu Nura saiyaji yakara jin dadi da natsuwa dakuma hamdala da auren Ummi dayayi da kyar Ummi ta iya sakinsu cikeda dabara tace “ga Dadyn ku bakumai oyoyo ba” sakin Ummi sukayi da sauri sukai wajen Dadyn su Ummi kuma tazo wajensu Hajiya ta duka ta gaishesu bayan anyi gaishe gaishe aka kawo abinci sukai nak Nura yafita sallan la’asar itama Hajiya tace bari nayi, Ummi taje ta cewa Meena pls Meena je mota ki bude akwatina akwai wani leda shine a saman kayana ki kawomini abin Hajiyane” murmushi Meena tayi tace “nifa” dasauri tace “naki na handbag dina” wucewa Meena tayi tafita bata wani jimaba takawoma Ummi ummi ta karba Meena tace “je daki ki kaimata mana kina kuma jin kunya ni natafi kitchen” wucewa Meena kitchen tayi Ummi tawuce dakin, Hajiya na zaune kan dadduma Ummi tayi sallama Hajiya tace “shigo mana Ummi aiba saikin jira nace ki shigo ba shigo shigo maza” dakin Ummi tashiga har gaban Hajiya ta duka akunyace tabama Hajiya ledan tace “Hajiya ga tsaraban dana yo miki ba yawa” dasauri Hajiya tazaro idanu tace “laaaaaa Ummi harda wani yimini tsaraba ikon Allah, toooo Allah yayi Albarka Ummi, Allah yakawo kazantar daki” bude ledan tayi wasu manyan atampopi ne guda biyu akwatin nan da Nura yakawo gida ranan kayanta ne daya sayomata su kafin yamata proper akwati, an dinka wasu some baa dinka ba amman tadauko atampopi wayanda sukafi kyau aciki guda biyu, tasama Hajiya wani soft silipas dan madina blue da ake saidawa akauyensu tasayo, da irin dankwalayen nan na tsofaffi kallabi masu kyau guda uku daban daban, ga mamakin Ummi sai kawai Hajiya tafashe da kuka sosai tana kallon kayan tace “Ummi ni kikasiyoma duka abubuwan nan”? Adan tsorace Ummi ta kalleta danta tsorata kartaga kaman ta rainata tanada yara masu kudi yarta na Egypt amman tazo tana mata kyautan danmadina, sai kawai taga Hajiya tahau kwalama Meena da matan baffansu kira dasauri suka shigo cikeda kukan farin ciki tace “Karime, Meena ku kalli abinda yarinyar nan tasayo mini, babu wanda yataba siyamini tsaraba irin wannan daya faranta mini rai haka, nadade ina neman dan madina sabida ciwon kafana kinsan takalmin da laushi duk silipas da ake sayomini saidai nasa ba yanda zanyi, jibi kalluba ku kalli atampopi na, Allah miki albarka Ummi, yanda kika faranta mini ubangiji Allah ya fara tamiki” sai kawai sukahau yima Ummi godiya akunyace ta tashi tafita Meena tabiyota sukaje dakin da Meena ke kwana sai Meena taji takara sonta sabida yanda tasaka Hajiya farin ciki kuma tai alkawari zata kira su Ya Aisha dukta fadi musu dudda tasan ma Hajiya zata fadi, dan babu wanda bazaiji labarin kyautan nan ba yau haka Hajiya taje bata boye abin arziki. Nura na shigowa gidan Hajiya tace “Nura kalli tsaraban da matanka tayomini ohhh Nura yarinyar nan Ummi saidai Allah ya yimata albarka kawai, kasan yanda silipas din nan da kalluban nan sukamin dadi kuwa, gashi yamin chass akafa, achan achan Masha Allah kaga kiramini kanwarka Aishaa nagaya mata abinda matarka tamin” yana xaune nan yana taya Hajiya dialing numbers saida takira yaranta uku mata ta gayamusu sukace asa Meena ta tura musu lomban amaryan Ya Nura duk zasu kira sunata godiya. Yanda Hajiya ke murna tana fadama kowa kyautan nan sai shiwa Ummi albarka take bakaramin dadi Nura yaji aranshi ba yana kallon atampopin, shine yasayo su anan Adamawa abinda yafi bashi mamaki yanda sunfi kowani atampa kyau cikin kayan daya sayo mata, design nasu is so beautiful but suta dauka tabawa Hajiya kuma wlh bata fadamai ba, baimasan tana tareda takalman nan ko kallbin nan ba that means tun akuayensu tasayo, kawai saiyaji yakara respecting yarinyar imagine ko shi baisayo musu tsaraba ba shi dama ansanshi baya tsaraba bai iya riko tsarababa amman yatashi sayo abu zai shiga super market ya jido kaya, abin really touched him bazaima iya misilta dadin dayaji ba, duk wanda zai tayashi da Hajiyan shi farin ciki babu abinda bazaima mutumin ba cus Hajiya number 1 ce arayuwanshi. Zama yayi abinshi tareda Hajiya anan dakin nata sunata hira bini bini ta shiwa Ummi albarka har abin yasa yasomajin kishi maisa shima bai kawo tsaraba ba yasami kalan addu’an nan da Hajiya kema Ummi haka? Kawai abin saiya zama kaman eye opener dagayau duk yayi tafiya kobaiso saiya sayo tsaraba yakawo shima In sha Allah Ummi takoyamai something in this his old age. “Ka sanarda Hadiza kayi aure Nura?” Dasauri yadago kanshi daga katifa yakalli Hajiya jin tambayanta ganin yayi shiru yasa tace “baka kyautaba Nura ai kome Hadiza tamaka ba’a haka, bai dace kawai taga mata daga sama ba dan haka ka sanar da ita yau, sannan ka kira kanwarka Aisha ko ita ko Maimuna ko Matar Baffan ka Karemi kabasu kudi ahadoma Ummi da Hadiza akwati, sannan kaji tsoron Allah kayi adalci atsakanin su dan rashin yinsa zai kaika wuta, ka manta duka halin Hadiza na baya ka bude sabon chapter yanzu and treat them equally kada ka cutar da Hadiza sannan kada ka bari ta cutar da Ummi dubada tafita wayewa dakuma shekaru, sannan kada kabari Ummi ta raina Hadiza ganin itace amarya ko ka nuna mata kafifitata kan Hadiza, kada ka kuskura ka rike matanka ahaka kowacce ka rike sirrinta azuciyanka kada ka sanar da Hadiza kanada matsala da Ummi haka kada kasanar da Ummi kanada matsala da Hadiza, ka kama girmanka kayi tsayin daka akansu, ka tsare hakki dakuma mutuncin kowa kanajina Nura” Gyadamata kai yayi ahankali yace “naji Hajiya” kanshi ta shafa tace “kayafema Hadiza kome tamaka kada ka riketa da laifinta please sannan yau karaba musu kwana, tunda baka gari kuma duk kana tareda Ummi ne lokacin yau kashiga dakin Hadiza kajini”? Gyadamata kai yayi yace “naji” ahankali tace “Allah yamaka Albarka Nura, yanda kake kulawa dani dinnan ka tsaya akan lamarina, kabani ci kabani sha kamin duk abinda nakeso sannan kaji magana ta Nura ubangiji Allah ya saka mata da aljanna” murmushi yamata yace “Ameen Hajiya nagode” murmushi tamai tace “idan naji sauki komi ya tabbata saika gana da yaron dake neman Auren Auta ko”? Gyadamata kai yayi yace “eh Hajiya amman tana aure xakibar kano ki dawo gidana da zama bazan barki ki zauna ke kadaiba gaskiya” dasauri Hajiya tace “kai barni da Abujan nan wlh ba sonta nake ba nafison kano” dasauri yace “Hajiya akwai flat dinki daban agidana, nan da wata biyu za’a gama komi bazaki zauna ke kadaiba a kano gaskiya” ahankali tace “to baridai lokacin yayi sai muyi wannan maganan, tashi kaje masallaci an tada salla leka min Meena da Ummi kagani Allah sa sun tuna sun hada kayan su Amal ba sun tsaya hira ba” wucewa tayi yafita dakin da Meena take yaje yadaga labule yayi Ummi kadaice adakin tana shirya kayan su Aman bama tasan da zuwanshi ba sai aikin take harta ga Amal zaune gefenta hannunta da tuwon madara tanasha dan murmushi yayi akan Ummi yasoma sanin akwai wacce zata iyaso yaranka tsakani ga Allah koda ba ita ta haifesu ba saidai basu da yawa a duniya, gyaran murya yayi dasauri Ummi tadago kanta ta kalleshi folding hannu yayi akirji yace “awanki nawa baki sani a ido ba”? Murmushi tayi kaman mai tunani tace “uhmmmm awa biyu da minti ashirin da uku da sakan shidda kenan bansa Dadyn Amal a idona ba” dasauri yace “shine kuma kike murmushi” hadiye murmushin tayi tace “tuba nake nadaina Yallabai” kwafa yayi yace “kinci sa’a akwai Princess anan” dasauri tajuya taja hancin Amal tace “ai princess zaki dinga cetona koda yaushe ko?” Amal tace “yesssss Anty Ummi na” dariya tayi takalleshi tace “kaji ko” hararanta yayi yana murmushi yace “kuyi salla ku shirya nadawo zamu tafi” gyadamai kai tayi tace “to mijina, adawo lafiya asamu a addu’a fa idan kana cikin jam’in nan kaji” juyawa yayi yace “naji matata” yayi murmushi yawuce Meena tazo da gudu tace “ke Ummi haka kuke soyewa keda Yayana, zona koya miki zama da Hadiza……..” Yana dawowa aka zuba komi a mota harda abincin dare Hajiya tasa Meena tazuba musu a babban kula dantasan matan gidan bata dafaba kuma bazatazo Ummi tahau aiki da daddaren nan ba suka musu sallama suka tafi saida ya tsaya yayi salla ma………. Parking motarshi yayi Ummi taji gabanta yafadi kallon gidan tayi takasa fitowa su Amal dake tareda ita sukace “Anty Ummi muje gida” daidai lokacin Nura na bude musu baya yakalleta suka hada ido yace “muje” gyadamai kai ahankali, ganin yanda tayi yasa yamika mata hannunshi ahankali takama yafito da ita sannan yadauki Amal itakuma takama hannun Aman gateman namusu sannu da zuwa yana bude boot na mota dan kwaso akwatinan su, bude kofan falon Nura yayi ahankali da sallama abakinshi Hadiza na zaune kan kujera daga ita sai wani material data saka na batic mai shegen kyau gown yana walkiya walwal kyau purple hannunta rikeda wayanta dake kunne tana magana ga MacBook nata kan cinyanta tana aiki tadan saka farin reading glasses a idanunta kanta da kalaba yan kananu ganin Nura rikeda Amal yasa dasauri tace “I will call you back Hajar just send the order ta IG ko WhatsApp me” takatse wayan dasauri tayi tana kallon Nura dashima yake kallonta batare datacemai uppan ba dan fushi take dashi sosai sabida abinda yamata, shigowa Nura yayi saikuma yajuya yakalli Ummi data tsaya gaban kofan batare data shigoba Nura yace “shigo” gyadamai kai tayi tashigo ahankali kanta akasa tana rikeda hannun Aman Hadiza tabita da kallon mamaki irin mugun mamaki daidai nan Gateman na shigo da akwatinan su yabarsu anan falo yawuce yafita bayan yagaida Hadiza dako kallonshi batayi ba balle yasaran zata amsa, ahankali Ummi kanta na kasa tace “ina yini Anty” har lokacin Hadiza kallon Ummi data chanza mata take a ido sosai ganinta tareda mijinta a ina yaganta? Taya suka hadu? Tayaya suka dawo gidan tare? Yarinyar dake kauye? Yanda tambayan ke cinta arai yasa batare data amsa gaisuwan ba tace “meya hadaki da mijina dakuka shigo gidan tare ko ince kuka dawo gidan tare? Kumama bance kada ki kara dawomin gida ba tunda kin tafi ganin kakarki nariga nakoreki, na sallameki me kike dawo yimini agida kuma sannan kika shigo tareda mijina”? Sauke Amal Nura yayi yakalli Aman yace “kuje dakinku asama kujira gani nan zuwa” dasauri Amal tace “Daddy zakazo ka karanta mana stories?” Gyadamata kai yayi dasauri sukai stairs suka wuce sama without saying a word to Maman su kaman ma bata falon. Dudda Nura yaji ciwon ko gaidashi batayi ba balle amsa sallaman dayayi ko cemai sannu da zuwa batayiba amman saiya daure yakalli Ummi yace “zoki zauna nayi magana daku” Ummi kanta na kasa ta taho Hadiza jitayi jikinta da kafafunta sun fara rawa hakan yasa tasauke MacBook nata dake kan cinyanta ganin wani attention da care da Nura kebama Yarinyar nan wanda bata taba ganin yayiba tsawon kusan a year datake aiki agidansu, shida ko kallo yar aiki bata isheshi bama, ganin Ummi takasa motsi yasa Nura yazo da kanshi ahankali yakai hannunshi yakama hannunta dawani kalan sauri Hadiza tamike tsaye tana kallon Nura dataga yariko hannun Ummi, shigowa da Ummi yayi cikin falon yazaunar da ita kan kujera shikuma yazauna kan 1 sitter yana facing nasu yakalli Hadiza dake tsaye yace “sit” cikin bugawan kirji trying to calm herself down but takasa sabida yanda kirjinta ke tafarfasan bala’i ganin yanda yakamo hannun yar aikinta tace “Nuri just say abinda kakeso kafadi basaina zauna ba cus I don’t understand sa yar aikin nan zama kan kujera na dakayi kana rike mata hannu, maganan me zakamin eh”? Sosai Nura ke kallonta ganin rashin mutuncin ta da rashin kunyanta na nan dudda yadan punishing nata kwanan nan saikuma anatse yace “Hadiza Ummi ba yar aiki bace yanzu, naje har kauyensu na nemi aurenta an bani, yau kwana goma sha hudu da daura mana aure! Ummi is my wife!”. Today da Matan Auren gidan nake when was the last time kika daga waya kika kira Maman mijinki just to say Hi Mama yakike?? Makesure kin kira yau🥰 Idan kuna gari daya when was the last time taci abincin ki?? Yau weekend yi lafiyayyan girki ki aikamata 🥰 When was the last time kika siya mata gifts? Kikai making nata happy?? Do that yauma😎 Ance akwai a thousand ways to zuciyan miji and one of those ways is when you carry his Mom asaman kanki, lokacin dazaki dinga kula da mahaifiyarshi kaman taki.❤️ Like I said still yau zan fada this book badan fun ko dadi nayi ba nayishi ne for US maybe this book yarage rate na divorce da ake samu Kwanan nan agidajen aure. Everything in this book is a lesson not just the kishiya part, zamantakewa, kyautatawa, soyayya, yara da sauransu duka nakawo.❤️ I have a question for Mamas, duba da maganan na batai failing as a Mom ba cus tana sayama yaranta heaven on earth and tabasu the best yar aiki dasuke so inaso naji view naku kuna ganin GIFTS kesa yara su shaku da Mom nasu ko spending quality time dasu?? And is it possible yara su fison wacce ba ita ta haifesu ba kan wacce ta haifesu???? Maisa Aman and Amal prefers Ummi to Maman su????? WEEKEND PROMO💃💃 I have special announcement masu son shiga class na MATAN AURE you can all pay 1k now kafin Monday yakoma 2k, registration is still ongoing kafin murufe. 🔊🔊🔊🔊🎊🎊🎊🎊🎊 Don’t miss MATAN AURE dina class for anything, I will give you all!! Sirri zan baku da dama Zan koya muku how to love mijinki in your own way kaman yanda Ummi keyi. Shagwaba, iya magana 🥰 Uwa uba iya kwanciya❤️, yanda ake siyan zuciyan miji, how to steal heart na Inlaws naki and so much more.😍 Idan kina tunanin asiri ko kayan mata ke siyan zuciyan miji come to my group na nuna miki gaskiya. HAUSA CLASS NE BA TURENCI BA REGISTRATION IS 1k NOW 6353995766 M Shakur world Moniepoint Send ur evidence of payment ta PC zanyi adding naki a group. click on this link and chat me up directly wa.me/+2347012181461 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣2️⃣ Ga KAYAN MATA PLUG nakawo muku. Ummu Fua’d tahada wasu lafiyayyan magunguna kaman su Shu'umar humra Bita zaizai Matar so Alajab Na tsugono Al oud special na kaya Mowar mace dashi zata turara jikinta Sai till we meet ruwan wankane a toilet dinta Night queen shi take shafawa da daddare Makhmaria tana shafawa ajikinta Sunshine kuma shi take shafawa angon a inner wears tana turare masa inner wears dinsa da turaren matar so. Just chat her up koku shiga group dinta💃 ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/Izv1KgHEcNl5uwqalMM9Oe Episode 12 Wani irin kallo Hadiza kema Nura kaman wacce hankalinta ya gushe ta tsare bakinshi da yanda labbunshi ke motsi da kallo kanta yayi wani dummmmmmmmmm, kunnuwanta sunyi wani shuuuuuuu kaman irin ana hura tsakiyan gwangwani kanta yamata nauyi kaman an daura block kawai kallon Nura take da bakinshi dake motsi, tanajin wasu maganganun wasuma bataji, anatse Nura yace “for now anan zamu zauna dukan mu kafin nan da 2month an gama gidana zamu koma kowaccen ku nada flat dinta, for now ita zata dauki dakina ke kina dakinki ni zai zamto banda daki, duk wacce yake girkin ta zan kwana adakinta wanda zan raba muku 2-2days, da zan iya daukan dayan dakin dake kusada naki but sabida baki gwara kawai ni nahakura da rashin dakin ai is just 2month or less ma, kece Babba Hadiza ga Ummi nan amana, Ummi kece karama ban yarda ki sabama Hadiza ba, kuyi zamanku lafiya nariga nabiya kudi yau za’a hadoma kowaccen ku akwati, sannan Hadiza ki duba gidan komene babu saiki sanar dani nakawo kinji” sosai Hadiza kecikin wani kalan state dabazata iya tantance kowani yanayi take ciki ba hakan yasa takasa magana shock yarufe mata baki, shi Nura har kasan ranshi yaji dadin shirun datayi dan baiso tai haukan nan agaban Ummi koma menene tamai shi adaki kokuma kawai dai not in present of Ummi dan baison abinda zaisa Ummi ta rainata, kallon Ummi yayi yace “tashi kitafi dakinki asama saida safe” gyadamai kai tayi tamike tawuce tana tafiya ahankali tayi hanyar staircase daidai ta daga kafanta zatahau bene cikin wani irin murya dashi kanshi Nura baisan Hadiza nada itaba tace “Um……….mmi!” Chak Ummi ta tsaya tareda juyowa dasauri gabanta nafaduwa, awani kalan zuciye Hadiza ta taho zatai wajen karaf Nura yarike mata hannu yace “ina zaki” cikin wani buhun uban ihu Hadiza tace “sakeni Nuri kafin na daukeka da mari, tell yar aikin chan tabarmini gidana right this minutes dan I just want to assume all abubuwan dakagama fadi yanzun nan wasa kake is a prank Nura, let’s pretend you are just joking, baka isa kamin kishiya ba Nura, Nuri nace baka isa kamin kishiya ba! Kai baka isa ka kara aureba Nuri! So tell this village girl to get out of my house right this minute before na salwantar da rayuwanta! Nuri ka gayama yar aikin chan tabarmini gida” Hadiza tai maganan tana tura Nura so kawai take ta fizge kanta taje wajen da Ummi ke tsaye gaban bene, “Hadiza!” Nura yakira Hadiza azafaffe yana rikeda ita ya jijjigata yace “look at me” juyoda kanta tayi from kallon Ummi datakeyi, kallonshi tayi da jajayen rinannun idanunta tana kallon cikin kololuwan idanunshi kaman yanda yake kallon nata yace “nakara aure Hadiza! Nayi wani aure Hadiza! And Ummi na aura! Na aure Ummi! Yes Ummi is my wife! Matata………” “Noooooooo!” Hadiza tayi wani kalan ihu da saida gidan yadauka tadaura duka hannayenta biyu akan kunnenta takara kurma ihu dako maigadi zai iyaji tace “nooooooo! Nooooooo! Nuri I said No! Yar aikin chan can never, ever become your wife!” saukowa su Aman dasukayi ji ihu yasa Nura yajuya yakalli wajen, wajen Ummi yaran suka tsaya tareda rikemata hannu Aman yace “Anty Ummi menene”? Nura na kallonsu yace “kaisu sama su kwanta Ummi” gyadamai kai tayi takamasu sukai sama dagudu Hadiza ta yunkura zatai wajen kaman mahaukaciya tace “karki sake kije saman gidana, zokibar gidan nan” dasauri Nura yariketa gam yakalli Ummi data dake tsayawa yace “go” wucewa sukayi yaran duksun tsorata ganin abinda Maman su keyi, Nura saida yaji karan sun rufe kofa sannan yasaki Hadizan, babu alamun wasa kan fuskanshi yace “Hadiza nakara aure because of so many reasons which I don’t wanna go into details of that dan kin fini sani, please ki kama kanki don’t start with this your drama” Nura yamata magana babu alamun wasa akan fuskanshi, Hadiza na wani kalan kallonshi da idanunta dasukai jazur ganin ya chanza mata kaman bashiba dan da dane tai abubuwan nan shareta zaiyi bazaimace wani abuba saikuma tadaga hannunta tanuna kanta muryanta yayi sanyi kaman kankara tace “Nuri ni? Ni? Wai ni Hadiza kama kishiya Nuri?? Nura!?” Takira sunanshi cikeda mamaki, shiru tasakeyi tana kallonshi tana kara kara kallonshi, sai kawai takai duka hannayenta ta kama gaban riganshi kaman akace ta dakeshi zata iyane tace “Nuri ni zaka yaudara haka da yar aiki na? My slave fa? Wacce kecin kashin gidana dana yarana? Yarinyar dani nakira agency aiki aka kawomini ita all u ever did was to pay salary nata, Nuri wai am I dreaming did u just say ka auri Ummi yar aiki na? Nuri wannan wani kalan bakin cin amana? Yar aiki na fa Nuri, Ummi, Ummi this Ummi dakemini gyaran gida da wanke baya da wanke wanke ita kaje ka auro?? Nooo I don’t believe this it’s a lie, Nuri wai ni Hadiza kama kishiya da yar aikina”? Yana kallonta yace “let it sink in your brain nakara aure, and yes yar aikin taki Ummi na aura haramun ne? Ummi is my wife now so cikani” sake chakumeshi HADIZA tayi da kyau zuciyanta na tafarfasa kaman ta mutu takeji tace “amman Nura kacika annamimin, makirin, munafuki maci amana da tsoron Allah, Nura wato all this while you’ve been fooling me kana soyayya da yarinyar nan kazo kasata tacemin zataje kauyensu duba kakarta kuka tafi kaje ka aurota, Nura yau 14days sau daya nayi magana dakai u don’t return my calls, u don’t reply messeges dina, Nura ni Hadiza kama kishiya wai Ummi, Ummi dai yar aiki na? Nizaka yaudara kaci amanata Nura, eh”? Hannunshi yadaura kan nata yacire daga gaban riganshi yace “bandawo gidan nan to fight with you ba so just respect yourself kidena haukan nan kar co wife naki ta rainaki” kaman ya zubama Hadiza fetur wucewa tayi stairs tace “durun uwan cowife, ita Ummi hartanada liver aure mini mijina? Wlh Nura auren nan trust me dream kakeyi baka isa bane kuma kayi kadan kamin kishiya na rantse mama da Allah sainasa gidan nan ya gagareta zama billahillazi la’ilaha illahuwa, babu macen data isa ta auri mijin Hadiza kai ko yar boko mata masu usuli da daraja basu isa su auremini mijina ba balle kuma yar aiki, mijina Ummi ta aura ni? Aiko tanaso ta mutu” da gudu gudu take hawa stairs daidai takai falon sama Nura daya biyota ya fizgota azuciye tai ihu tace “saken mini hannu Nuri” kobi takanta Nura baiyiba dakinta yabude ya jefata ciki yashigo shima tareda maida kofan yana rufewa yana saka key yazaro key ya jefa a aljihu dasauri ta taho wajen kofan tayi ihu tana dukan kofan da hannu tace “kabude mini kofa nafita I need to show that girl her proper place which is trash, wlh, wlh I will never share mijina da wata balle kuma Ummi yar aiki, kabude kofa! Nura open this door ko na fasa kofan nan” “Enough!” Nura yadaka mata tsawa da saida tadan firgita dan kaman zai daketa, nunata yayi da yatsa yana kallon kwayar idanun ta da idanunshi da sukai jajir yace “enough of your nonsense Hadiza! The only reason I even let you back into this house sabida Hajiya ne! Aure is not a do or die matter, idan kinga bazaki iya cigaba da zama amatsayin matata ba let me know I will let you go, but wannan haukan naki nagama dauka Hadiza your time is up, koki natsu and live peacefully under me ko u can leave the Marraige nagaji, nagaji da stupid, wild attitude naki always barking woo woo kaman karya haba! Don’t you get tired of shouting? Why do you think violence is always the way out for you? Kina behaving kaman ba mace ba, is something wrong with you upstairs I can take you to the asylum adubamini ke, nayi aure and so wat?” wani kalan kallo Hadiza kema Nura tunda ta aureshi yau kusan 10yrs kenan dan bata haihu da wuri ba yaune rana na farko da Nura yabude baki yamata masifa haka, bawai basa fada bane no sunayi but masifa ya kwakkwance mata haka yaune rana na farko, sosai take kallonshi Nura jikinta na bar-bar duk yanda taso ta daure ta cije tahana kanta saita kasa sabida yanda yakirata karya, harda mahaukaciya ma dan cewa yayi zai kaita asibitin mahaukata aduba ta, yana kuma threatening nata da rabuwan aure kawai saiga hawaye sharrrr ya sauko daga idanuwanta masu mugun zafi, muryanta babuma karfi balle kuzari tasake nuna kanta tace “Nuri ni? Ni kake gayama bakaken maganganu haka? Nuri nika tsana haka? U just called me a dog, mahaukaciya and so much more, Nuri you hate me sabida kayi aure? You hate the sight of me, Nura ni zaka cima mutunci ta hanyar auren yar aiki na? Idan ka tsaneni haka kagaji dani zaka iya cika ragowan saki biyun dasuka rage why marry maid dina? Kasan yanda nakeji azuciyana Nuri ni, kaci amanata, ka yaudareni, ka munafinceni” wucewa tayi dasauri taje gaban gado tazauna akasa ta kankame kanta tana shaking kaman ta haukace, saikuma tafara buga kanta ajikin gado jikinta ko’ina da bakinta na rawa tana maganganu. “yar aikina, yar aiki, Nuri ya auro mini yar aiki na, Nuri ya tsaneni, ya tsaneni, ya tsani ganina, ya cuceni, ya wulakanta ni, ya toxarta ni, Nuri zoka kasheni nasan bana duniya namutu kayi auren nan, aure fa? Aure Nuri yayi aboye sai yau bayan sati biyu yake fadamin kuma yar aiki na, Ummi, Ummi, Ummi uhmmm Ummi”. Nura kawai yayi shiru ya tsaya yana kallonta he can’t even remember the last time dayaga Hadisa na kuka haka maybe tun kafin aurensu, cus irin hard ass ladies dinnan ne ita, she’s in total shock dan bamatasan tana kukan ba, strong woman Hadiza ke kuka hakayau, he wanted to ignore her amman kuma saiya kasa ganin yanda take hitting kanta is getting serious sai kawai yawuce tabashi tausayi, kishiya koyaya batada dadi azuciyan mata but yazaiyi she pushed him yayi? Wucewa yayi yacire kayan jikinshi yarage daga singlet sai boxer, sannan yadauki wani bottle water daya gani adakin yataho inda take gently ya tsugunna agabanta ahankali yakai hannunshi yadaura kan fuskanta yana cire kanta daga jikin gadon dasauri ta kabarda hannunshi tana kuka wiwi komi najikinta rawa yake tace “kada kasake tabani da hannun nan daka taba wata, Nura nika yaudara haka kaci amanar alkawarin mu, Nura nizaka wulakanta ka tonama asiri ni Hadiza the mother of your kids, Nuri what have I done to you to deserve this eh? How can you comfortably hurt me this much? Nuri haka ka tsaneni?” girgiza mata kai yayi ya ijiye ruwan agefe ganin yanda jikinta ke rawa she’s seriously having a panic attack gumi na keto mata tana zufa duk kalan Ac dake dakin, ahankali softly yace “come here Hadiza, u are not in right state of mind yanzu kome nagaya miki bazaki gane menake cewa ba, zonan” da karfi yasata ajikinshi tana ihu kasakeni, sata akirjinshi yayi da karfi yana patting back nata kaman yakara cemata takara karfin kukan wani kalan kuka take kaman anmata rasuwa yacigaba da patting nata lovely yace “shiiii it’s okay” kankameshi Hadiza tayi sosai da sauri ita kanta batasan iyakan son datakema Nura ba sai yanzu dayay hugging nata kaman yana waking feelings din datake dashi for him she became so vulnerable and weak, yau batada karfin nuna she’s a strong woman dan zancen kishiyan nan hit her so damn hard, kuka take bana wasaba harda shesheka singlet din Nura ya jike sharkap da hawayenta, she’s just crying, crying bana wasaba kaman zata mutu takeji, wani luteten dunkulelen bakin ciki takeji bana wasaba, sosai Nura ke lallashinta ta hanyar buga bayanta yana manna mata few kissing agefen wuya like a baby, tana jikinshi cikin kukan tace “Nuri dan Allah kada kamin kishiya kaji, Nuri dan Allah wlh I can’t stand naganka da wata zan iya haukacewa barinma yar aiki na, dan Allah kaji Nuri mena maka zakamin kishiya da Ummi eh”? Yana bubbuga bayanta yace “Hadiza u are a very very stubborn woman, when I married u bahaka kikeba, I loved you kaman ba gobe you know, waye baisan kalan soyayyan damukayi ba, but everything changed damuka dawo garin nan, tunda na aureki baki taba cemin kinason kaza na hanaki ba, I change kayan daki anytime kikcemin kinason a chanza, I change cars for you, banwani damu da zuwa vacation ba but kinaso ke we go on vacation every year banda Umara da every now and then nake kaiki, have I ever wronged you kona hanaki abinda kikeso? Farko farko ai kinamin girki rana daya kawai kika ijiye, bakimin komi, baki damu dani ba nor my children wanda kinsan banda abinda nakeso aduniya kaman su, I can’t talk to you kafin nayi miki magana daya kinyi magana dari, kinamin ihu aka kaman yaron dakika haifa, bakiganin girmana ko darajata, Kona Hajiya, all I ask is for your attention and care, respect sannan kisa ido akan yarana but kin nuna ban isaba ban isa incemiki yi kazaba agaban idona zakice no, Bana iya tankwaraki ko kadan, u feel nidake daya ne, abu kadan kice feminism bazaki bari nayi demeaning naki ko belittling naki ba, you’ve been maltreating me doing as u wish, Hadiza ni ba yaro bane am 49 clocking 50 Allah yahoremini arziki da abinyi all I want yanzu is peace of mind and watch my kids grow na barmusu this company suyi taking over but kinki cooperating, u pushed me so hard and kinfi kowa sanina banda son mata banda biye biye, I’ve always been a one woman’s man but u made me look outside Alhamdulillah bantaba zina arayuwana ba and bazantabayi ba that’s the reason nakara aure don na sami kwanciyan hankali” cikin kuka sosai tana wani kalan sauke ijiyan zuciya tace “to saika auri yar aikina” Yana tapping bayanta har lokacin yace “Ummi ce the only macen dake rayuwana banda ke, kema kinsan ko kallo mata basu isheni ba, halinki made me notice the girl, yarinyar is a very good girl, she’s young, smart hardworking, she can cook and above all yarana na sonta sosai sais…….” jin zafin yanda Nura ke yabon Ummi yasa cikin kuka Hadiza tace “banson ji, toka saketa dagayau kome kace nayi zanyi please ka saketa na yarda ta kwana agidan nan yau gobe da sassafe tabar mana gidanmu I promise zan chanza kome kakeso zan maka amman kasaketa please Nuri karufamini asiri, I can cook nima, gani hardworking, smart, intelligent kuma I’m educated unlike yar aikin, kasaketa wlh zan chanza namaka alkawari” ahankali Nura yajaye jikinshi dagana Hadiza yakalleta batare dayace komiba, fashewa da kuka sosai tayi takai yatsanta ta taba harshenta tace “na rantse da Allah Wallahi Wallahi Nuri kaji na rantse ko kasaketa zan dawo sak Hadiza na nada, nadinga maka komi, bazan kara bata maka raiba, please karufamin asiri kada kasa duniya tamin dariya akaji ka auri yar aikina, please kasake ta kaji Nuri” dan lumshe idanu Nura yayi yabudesu yakalli Hadiza dake kallonshi tace “kaji Nuri kasaketa” girgiza mata kai yayi ahankali yace “bazan iya sakin Ummi ba Hadiza!” Dum! Gaban Hadiza yabuga dasauri harsaida takai duka hannayenta saman kirjinta wani sanyi na ratsata tace “mesa Nuri bayan nagaya maka zanyi komi infact nama gama daukan yar aiki har abada, dakaina zan dinga komi and take care of su Amal maisa bazaka saketa ba? U don’t need anything from her again, nice dama kuma nace zan chanza dagayau, maisa bazaka saketa ba”? Yana kallonta right in the eye yace “sabida nariga nakamu da sonta kaman yanda nake sonki!” Tunda Allah ya hallito Hadiza bata tabajin wannan kalan pain din datakeji azuciyanta yanzu ba jin mijinta nagaya mata da bakinshi cewa yakamu da son wata kuma yana gayamata right before her eyes wai bazai iya rabuwa da itaba sabida yana sonta kaman yanda itama yake sonta wato harya soma raba musu komi equally irin ita da yar aikinta duka abu dayane yanzu azuciyanshi, kawai saitaji kaman zuciyanta ya buga kawai tai baya luuu bawai ta suma bane tanaji sarai yanda yake kiranta da yanda yariketa yana shafa ruwa a fuskanta kawai her energy is just on a zero level idanma akwai minus zero energy level nata na wajen, kaman ya lura da hakan hakan yasa Nura yadauketa ahankali yadaura kan gado ya kwanta gefenta tareda kashe wuta ahankali ya rungumeta cikeda lallashi yace “I still very much love you Hadiza don’t hurt yourself okay, you are my first love Hadiza, Maman yarana, yaran dasuka zame mini haske arayuwana, u gave me the most beautiful, adorable and sweet kids aduniyan nan no one yataba bani kalan gift din dakika bani Hadiza how can I even hate you eh my Didi”? Bakaramin tausayi tabashi ba, wlh yayi auren nan but ko kadan baimayi tunanin kalan wannan reaction din zatayi ba he was just expecting haukanta as usual baitaba sanin she will be this down ba and weak tana kuka haka having panic attack hakaba, so dama tana sonshi, batason taganshi da kowace mace but shine takemai all abubuwan datake, lallai kishi babban abune awajen mata. Gently yadaura bakinshi kan nata hannunshi yana share hawayen dake fitowa daga idanunta yana kissing nata kafin ahankali yafara yunkurin making love da ita cikeda rashin karfi dakuma kuka cikin muryan bakin ciki tai ihuu tace “kada kasake ka sadu dani Nuri gabanka daya shiga jikin yar aikina bazai kara shiga jikina ba wlh kajini” hada bakinshi yayi da ita bai kara bari tayi magana ba dudda batada karfi saida tai kokawa dashi dan bataso yamata wani abuba but still saida yayi sexing nata da karfi da yaji she have no option but to succumb jikinta ya mutu gabaki daya kawai sai kuka takemai, dole ma Hadiza taso mijinta tayi kishinshi, Nura nada kirki ne sosai lallashinta yake bana wasaba yadinga shafa kanta duk uban bakin cikin datake ciki saida soyayyanshi yayi suppressing nashi bacci yayi awon gaba da ita sai ijiyan zuciya taje saukewa ajikinshi he cant lie is just soothing sex ne kawai wannan to calm her down dan sex na rage bakin ciki da damuwa, that fun da excitement dinnan ajikin Ummi kadai yakeji, lullubeta yayi da bargo yatashi bayinta yawuce yaje yayi wanka yafito kayanshi yasake maidawa yayi wajen kofa ahankali yabude yafita yaranshi yafara dubawa yayi mamaki ganin duk Ummi tamusu wanka sunsa kayan bacci tarufesu da bargo tarage musu AC addu’a yamusu yafito dakinshi wanda yake dakin Ummi yanzu yawuce ahankali yabude kofan tana kwance akan gado tai lamo dudda ba bacci takeba dan takasa bacci tun bude kofanshi taji, zama yayi ahankali bakin gadon yakalli fuskan Ummi feeling a bit bad cus baimata saida safe ba hannunshi yakai ya shafa kumatunta tareda dukowa ya manna mata kiss akai yace “good night Hajiya Ummi” sannan yamike yaje gaban wardrobe ya debi some clothes nashi yawuce yafito tareda rufe mata kofa yakoma dakin Hadiza hawaye Ummi taji sun gangaro mata daga ido kawai jitayi tana bama kanta tausayi most maganganun Hadiza tajisu dan maganan Hadiza ihu ne, maganganunshi ne batajiba but duk taji abinda Hadiza tafadi da cewa yasaketa datayi zata chanza shiyafi komi tada mata hankali saitaji takara raina kanta tana tunanin kodai Auren nan kuskurene, ita Allah yasani ba kwacema Hadiza miji tayiba babu wani mugunta aranta but tasan harga Allah dan bazata iyama Allah karyaba tanason Nura tana mutuwan sonshi, batajin zata iya rayuwa ba yasaketa ina! Tanason mijinta fa kome zatayi zatayi dan yazauna da ita karya rabu da ita, tuna yanda har kaman ya sadu ma da Hadizan dan taji Hadiza nacewa kada ka sake yasadu da ita da gabanka daka sadu da yar aikina, hawaye ne yazubo mata tasan ita yar kauyene bata waye kaman Hadiza ba sannan batai karatu ba but tanada hankali, sannan ta girma, ashirin da uku tana neman da hudu ba wasa bane, tasan menene miji sannan tasan banbancin miji mara kirki damai kirki, dan ta taba Auren mara kirki mugu yanzu yanda Allah yabata miji mai kirkin nan, wlh zatai kome dazatayi ta siye zuciyanshi takuma kara siye danginshi ta samanma kanta lafiyayyan wuri axuciyanshi, koda basuyi wani soyayya kafin aure ba yau alkawari takeyi zata samama kanta waje, bazata tabama Hadiza mugun abuba kawai dai bazata bari wani mahaluki aduniyan nan kap yarabata da Alhajinta bane, dan bata tabajin tanason abu kaman yanda takejin son Alhaji ba, yanda Allah yabata miji nagarin nan dare daya batare datai wani abuba bazata taba bari ya subuce mata ba tashigo rayuwan Alhaji tashigo kenan har abada Wallahi kuwa!. Tai maganan tana goge idanunta tasake juyi agado takasa bacci, sati biyun nan datayi tana kwana ajikinshi saitaji yau baccin ya gagareta, tashi tayi tafada bayi tafito daure da alwala tahau kan dadduma tayi salla tafara addu’a kan soyayyan ta da aurenta da Nura. Auuuucchhh I’m too emotional naso nacigaba but let’s take a moment of silence for our lioness Hadiza da Nura yay shattering ego nata today😎 Poor thing couldn’t hold back those tears 😭 ashe ta iya kuka😂 Auuu now I feel bad for HADIZA wlh, kishiya fa batada dadi but kuna ganin misali da Nura zai saki Ummi zata chanza???? Wai HADIZA ce ke kuka haka our strong fire for fire, feminist woman😂😂 Ummi dai tace taga miji, kuma tasamu gidan miji, zama daram injita mutuwa kadaice zata fitar da ita daga gidan mijinta Nura😂 Allah karabamu da kishiyoyi irin Ummi mayun maza😂😂😂 Anyway my people don’t forget to join MATAN AURE CLASS dina with just 1k today and tomorrow 💃 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣3️⃣ My people wai kunji labarin BUKKISH FABRICS N MORE?? Ku saurara kunji bantaba ganin masu harkan Atampas, laces dakuma lafiyayyun gangariyan ready to wear kaya ba dake badawa akan sari kwashakwasha kaman BUKKISH FABRICS N MORE ba, both wholesales n retails sunayi, sunefa akama taken PAY LESS STAY IN FASHION, wato ki biya kudi kadan amman ki saka kayan yayi adama dake, ku tura musu message now ku kwashi kaya with little kudi, danna link din nan kimusu magana👇🏼 wa.me/+2349034368170 Zaku iya duba shagonsu a TikTok- Bukkish fabrics n more 13 Wuraren 5 Nura yatashi daga bacci, Hadiza dake gefenshi yakalla har lokacin bacci take, sauka daga kangadon yayi yawuce bayi, wanka yafito ya shirya cikin wani jallabiya yana zuba kamshi yazo gaban gadon yadago Hadiza like a baby softly yace “jekiyi wanka kizo kiyi salla My Didi” bude idanunta tarr Hadiza tayi takalleshi yamata wani irin kyau yau saita ganshi yafi koda yaushe kyau dasauri takai hannunta tadaura kan fuskanshi tana kallonshi everything is coming back to her daya faru da ita jiya, cikin murya mai raunin gaske tace “Nuri mafarki nayi ko? Ai baka auri Ummi yar aiki na ba ko”? Dan murmushi kadan Nura yayi yakai hannunshi yacire hannunta dagakan fuskanshi yace “tashi kije kiyi wanka kiyi salla Hadiza” yana maganan yawuce yabude kofa yafito dakin Ummi yabude yashiga bata kan gadon harta gyara gadon, yabi dakin da kallo komi a gyare tsaf jin karan ruwa abayi yasa yaje gaban bayin ya tsaya tareda knocking cikin cool voice yace “wankan me kikeyi? Mafarkina kikayi?” Ummi nacikin bayin akunyace tace “wanka kawai nakeyi, ina kwana Mijina dafatan kayi bacci mai dadi kuma katashi lafiya?” Dan ijiyan zuciya Nura yasauke ahankali, he loves how Ummi always greet him, gaisuwa takemai not common gaisuwa but gaisuwa mai dauke da details, baki yabude zaiyi magana saikuma yace “ba’a magana abayi, maza kifito kiyi salla natafi masallaci” “uhm Uhm” tafadi amatsayin amsa hakan yasa yayi murmushi yace “naughty gurl” wucewa yayi yasauka kasa, yau monday he wants to see Hadiza ta chanza, he wants to be miji mai adalci, he just pray and hopes Hadiza will cooperate which he’s highly doubting it, dan yau girkin ta yakamata ita zatai girkin breakfast dasauransu, ijiyan zuciya kawai yasauke yatafi masallaci he’s just hoping zai dawo yaga tayi dama ga gidan na bukatan gyara. Bayan Ummi tayi salla wani lafiyayen super tadauko tasaka cikin atampopin daya dinka mata dogon rigane fitted tazauna gaban madubi ta shafa hoda tasa kwalli tashafa wani pink janbaki sannan tayi dauri bayan tasaka dan kunne, shiru tayi tanason tafita taje ta daurama yaran nan girki zasuje school but tana shakkan Hadiza deep down kuma tasan idan tabari babu mai musu at the same time tana tsoron kada ace tayi shishigi bayan yau girkin Hadiza ne amman kuma tanaso tanunama Hadiza bawai dantaci mutuncin ta ta auri Nura ba ita kawai tanason Nura ne, kusan 3min tayi ahaka sanan tabude kofa kaman munafuka tafito ta maida kofan tarufe batare data bari yayi karaba tawuce tasauka kasa falo tafara gyarawa agurguje da dinning ta tattara duka kwanukan cokalan tawuce dasu kitchen tashiga hada abincin gida tanama Hajiya girki tana gyara kitchen din duka at the same time. 6 Nura yashigo gidan yau bai wani zauna a masallaci ba dan baiso Hajiya tafito daga daki ta nemi Ummi da bala’i, falon daya gani harya chanza kama yasa yayi shiru dan kawai ranshi yagayamai Ummi ne barin dayaji motsi a kitchen kitchen din yawuce a kofan ya tsaya yana kallonta tuwo take tukawa, ahankali yashiga cikin kitchen din dasauri Ummi tajuyo jin motsi ganin Nura ne yasa tayi murmushi tace “Sabahal khayri Baban Amanu” takowa yayi yazo inda take sai kawai ya rungumeta ta baya yana shakan kamshin datake yayi shiru itama saitai shiru tanajin saukan ijiyan zuciyanshi, bai damu dadan zufan datakeba ya goga gefen fuskanshi anata kaman mai whispering yace “maisa kika shiga kitchen yau ba girkin ki bane”? Dan shiru tayi kaman bazata ce komiba cikeda hikima tace “Anty tana zuwa aiki ni bana aiki, shine nace bari nafito nakama mata ta hanyar yin abincin kari saikuma inaso nama Hajiya girki dazataci kafin ta tafi asibiti, tunda nadawo nizan dinga mata abinci, ita nakema tuwon alkaman nan” shiru Nura yayi yana rungume da ita abayanta, akwai wani kalan hikima da Ummi kedashi da wlh ko educated mata dasaukai karatu daidaikune kedashi, yarinyar is good with words, Ummi is smart, tanada broad hikima kan zaman aure wanda yasan aikin Gwaggon tane, yanda ta tashi da safen nan tanama mahaifiyarshi girki abin warm his heart, dago kanshi yayi ya manna mata peck akumatu yace “godiya nake Hajiya Ummi” dasauri tace “nika dainamin godiya dan nama Mamana abinci” murmushi yasakeyi saikuma kawai yasaketa tareda juyoda ita yayi hugging nata so tight yace “thank you Hajiya Ummimy na” akunyace tazare jikinta daga nashi tace “tuwo zai kone” murmushi yamata sabida baiso tai wani abun yace “bari naje natada yaranki namusu wanka na shiryasu” dasauri Ummi tace “kabarshi zan musu zansa sanwan miyane nazo sama” girgizamata kai yayi yace “aikin zai miki yawa just do the cooking zan musu wankan” yawuce kofa saikuma yajuyo yace “kimini shayi” gyadamai kai tayi tace “angama maigidana” murmushi yayi yabita da kallo kaman yazo yamata wani abu saikuma dai yadaure yafita dan murmushi Ummi tayi dudda tanada damuwa tana cikin shakku da fargaban karya saketa bazata taba nunamai ba tama kanta alkawarkn nan. Nura na zuwa sama baimaje dakin Hadiza ba dakin yaran yaje direct Aman yafara tarawa yakaishi bayi yasamai brush sannan yafito yaje dakin Amal yadauketa yakaita bayi yamata brush da wanka yafito da ita da towel yakoma dakin Aman yamai wanka shima wlh aikin yara is not easy yafito dashi da towel ya kwashi kayanshi sukazo dakin Amal anan yashiga shiryasu sunamai hira yana wasa dasu. My people wai kunji labarin BUKKISH FABRICS N MORE?? Ku saurara kunji bantaba ganin masu harkan Atampas, laces dakuma lafiyayyun gangariyan ready to wear kaya ba dake badawa akan sari kwashakwasha kaman BUKKISH FABRICS N MORE ba, both wholesales n retails sunayi, sunefa akama taken PAY LESS STAY IN FASHION, wato ki biya kudi kadan amman ki saka kayan yayi adama dake, ku tura musu message now ku kwashi kaya with little kudi, danna link din nan kimusu magana👇🏼 wa.me/+2349034368170 Zaku iya duba shagonsu a TikTok- Bukkish fabrics n more Nan da nan Ummi tagama abincin Hajiya tahada breakfast tasoya chips ta sossoya eggs da sausage ta hadama su Amal abinci a lunch bag tadauko tafito zata ijiye a dinning tahada ido da Hadiza dake tsaye a dinning din tana sanye da riga da wani palazzo trouser mai shegen kyau na material pink tayi folding hannunta a kirji tana kallon Ummi da jajayen idanunta dasuka kumbura sukai jazur kaman mai ciwon ido abinku da faran fata, chak Ummi ta tsaya anan gaban kitchen din takasa karasowa dinning din ayanda zuciya ke diban Hadiza jitake kaman tazo ta shake Ummi tamutu gabaki daya, daga kafanta tayi tafara tafiya ahankali akuma zuciye tace “how dare you Ummi kika aure mini miji? Ni Hadiza kika aurama miji? Kin manta lokacin dana taimaka miki kina neman aiki ido rufe wayanda kikema aiki ada sunyi japa sun koma Canada anata gantali dake a Abuja ana nema miki gidan aiki baki samuba, na taimaki rayuwanki nabaki aiki nakuma biyaki da kyau, yan aiki da ake biya duba ashirin, dubu shabiya but ni nace zani dinga biyan ki dubu hamsin sabida duka gidana zaki kula dashi da yarana sabida bani zama ina fita aiki, sakkayan dazaki mini kenan ki aure mini miji, mijina Ummi? Nura na?” Ihu Hadiza tayi tana tafiya tace “ki daga fuska ki kalli kwayar idanuna bakar munafuka, algunguma, makira bakar mayya, butulu, shedaniya watsassiya, sai bayan kin aureshi zakizo ki kasa kallona kina sunnar da kanki kasa kaman baiwar Allah, dagakai ki kalleni Ummi, nace ki kalleni!” Hadiza tai maganan tana ihu daidai tana kaiwa gaban Ummi ta finciko gaban riganta gamgam tawani kalan jijjiga Ummi ta mugun makureta tana kallon fuskanta tace “wulakantacciyan yarinyar irinki harta isa ta aure mini miji, ni Ummi kina yar aiki na, sabida ina fita na barmiki gida kikai using opportunity nan kika auri miji na eh”? Hadiza tai maganan tana buga Ummi abango saida Ummi tasaki lunchbag din kasa tai kara Hadiza ta makure mata wuya tace “wlh, wlh, yau saidai afutar da gawanki ki daga gidan nan, ke! Dakikiyar yarinyar irinki tayi kadan tace inyi kishi da ita, bazan taba iya raba Nuri dakowa ba balle ke jinjiran yar iska kinajina? I will kill duk wacce tace zata auri Nuri na, dagani sai shi har lahira” “Hadiza!” Nura daya sauko tareda yaran suna surutu ya hangosu da gudu gudu ya sauko daga bene yazo wajen da sauri ya bambare hannun Hadiza daga wuyan Ummi yace “are u mad kasheta zakiyi”? Tari Ummi tahauyi sosai tana nishi idanunta sunyi ja, cikeda fada Hadiza tasake yowa kan Ummi tace “Nuri ba ruwanka awannan fadan is between me and this this munafukar makiran yarinyar” dasauri Nura yatura Ummi bayanshi daidai su Aman suna zuwa wajen da gudu zasuyi wajen Ummi suna “Anty Ummi sorry” rikesu Hadiza tayi dasauri tana tafarfasa tace “ku zonan ina zaku?” Dasauri Aman yace “wurin Anty Ummi, u hurt her Mom” cikin ihu Hadiza kaman zata make Aman tace “waye Ummi? Me kuka hada da ita? Who is that girl to you? Dagayau baku ba ita Aman kaida sister ka, Ummi is a bad evil person, babu wanda yataba cutata arayuwan nan kaman ita, bantaba nadaman abu arayuwana kaman nai nadaman ranan dana dauketa aiki ba, kar wanda yasake kiran sunanta cikinku agidan nan, Ummi is the worst evi…….” “Hadiza!” Nura yasake kiranta ranshi abace dasauri Hadiza takalli Nura tace “what!? Nura I said what kake kirana? Don’t tell me ka yarda cewa yar aikin nan son yarana take? Okay bakaso nagayama yarana she’s evil, Lemme tell you something today Yarinyar nan bata taba son yarana ba, she just use them tayi winning heart naka da nawa damuka yarda ta zauna gidanmu, bata taba son yarana ba, she use them taja ra’ayinka kasota, tunda ta kyallara ido taga muna biyanta 50k instead of 20-15k da ake biyanta a inda tabasa aiki ta kudurci aniyan saita aureka, saita zama matarka, saisa taja yaran jikinta sabida tasan you love yarannan morethan ur life sune the way to your heart, your weakest point Nura, open your eyes and see Ummi played you and me, Nuri Mezakayi da this village evil girl yar aiki fa eh Allah kadai yasan mazan mutane nawa taci, I will post her pictures on social media to makesure babu wanda yakara daukanta aiki a abujan nan tunda she’s a witch, ka barni naci bura’uban yarinyar nan Nuri tasan cewa Allah dayane” Hadiza takaima Ummi nushi Nuri yatare hannu ta hanyar rike hannunta gam cikin kakkausan murya yace “karkiyi kuskuren tabamin mata Hadiza stop all this thing!” Nura yayi ihu saikuma cikin turenci yace “I’ve given this respect leave this girl alone before I disrespect you in front of her” tafi Hadiza tayi tace “akwai disrespect daya wuce na kariga ka aurota ka kwanta da yar aikina taga kalan buranka dani uwar dakinta keci akwai Eh Nura talk!” Hadiza tai ihuu dayasa Nura ya runtse idanu yabude su ahankali yakalli Aman da Amal daduk ke kallon Maman nasu sunyi tsuru tsuru, dan juyowa kadan Nura yayi yakalli Ummi dake labe abayanshi yace “tafi dakinki” gyadamai kai tayi tawuce Hadiza zatayi kanta Nura yariketa gam, Hadiza tabita da kallo tana duramata ashar tace “munafuka, jibeta kaman bushashen kifin dayay kwantar a kasuwa oporoko, banda ma namiji kanshi kaman kan jarirai ne mezakayi da yarinyar nan mai kama da fiffiken kunkurun dayay shekara dari da uku aduniya eh, makira zuciyanta yafi fatar jikinta baki, tanaji da lebe kaman wacce ke aiki agidan giy……” “Hadiza!” Nura yayi maganan yana fizgota su Aman suka fashe da kuka Nura yakalli yaran saikuma yasaketa yace “look at yaranki ko breakfast basuyi ba zasuje school kina haukan nan bakisan zaiyi affecting mental health da cognitive development nasu ba” cikin fushi tace “eh bazasuyi breakfast dinba ka gayama yarinyar chan bata ba yarana, kada ta kara dafa musu abinci kota musu wani abu, wlh ko hannunta nagani akan jikin yarana kome namata ita taja and kada ka ta kara shigan mini kitchen” Nura yana wani kallonta yace “kitchen banaki bane, duk wani abu naki na kitchen din nabaki dama ki kwashe ki ciresu daga kitchen din zan sayo wasu nasa cus Ummi will enter this kitchen and cook for me” Nura yakallesu yace “zo kuyi breakfast” rike hannun yaran tayi tace “Nura bari kaji yesterday you took advantage of my fragile state kayi yanda kaga dama dani not anymore, billahillazi Nura zan nuna maka cewa yimini kishiya was the worst mistake daka tabayi arayuwan ka, bakana fadin bakada kwanciyan hankali ba yanzu kafara ganin asalin rashin kwanciyan hankali, muzuba nidakai I will deal with you and deal with that thing daka kawomin gidan nan as matan ka, bakasan ba’a wasa da fire ba because u will get burn, Nura I will treat you f*ck up wallahi kuwa” sosai Nura ke kallon Hadiza but sabida yaran saiyayi shiru yatako har gabanta yaduka yakama Aman da Amal dake kuka looking terrified ya karbe su daga hannunta yace “bani yarana” yajuya zaiyi dinning dasu kafin yaje Hadiza tarigashi zuwa dinning din duka abincin da Ummi takai dinning dan breakfast Hadiza ta kabar, dasauri Nura yaja Aman baya dan yadauki Amal gudun karya kone da ruwan zafi yana kallon Hadiza, ahaukace ta duka ta kwashi lunchbox na yaran da Ummi ta watsar akasa dataji shaka dazu ta bude tana ciro komi tana zZzagewa akasa tace “baza’a aci abincin yar aikin ba, yarana bazasu karacin abincinta ba, nace baza’a ciba, angama cin abinci again, Nura that peace dakace bakasamu dani ba ajikin yar aikina zaka samu wlh, wlh, wlh bazaka sameshi ba, Nura u will never know peace now dakamin kishiya I swear by Allah” sosai Nura ke kallon Hadiza kaman ba itane tagama kuka jiya kaman wacce ke shirin mutuwa ba, baice mata komiba yajuya yakoma falo yazauna yaciro wayanshi yakira school din yaran yace abasu breakfsat da lunch yau daidai motan school din zuwa, lallashin yaran yayi yadauko juice a fridge yabasu sannan yafita yasasu a school bus sannan yadawo cikin gida Hadiza na tsaye a tsakar falon tarike waist nata tan kallon Nuran. Baiko kalleta ba yawuce zaiyi stairs tabishi da sauri tana ihu tana surfafa masifa tace “bakaji kunya na ba sabida kaine babban munafukan mazan duniya, Nura the president of MMA! Mugayen Maza Association, zaka kama ka auremini yar aikin dana samo nakawo gidan nan, kabita har kauyensu ka aureta kaje kayi honeymoon da ita batare daka dauki wayana ba for that 2weeks, shine kanada audacity kazo da daddare ka lallabani kana samin jikinka ajikina jikinka daya hadu dana yar aikina eh Nura? I looked up to you kullum as a role model cus Nadade banga namiji mai hankalin kaba, but I was wrong gaskiyan bature ne dayace a fool at 40 is a fool forever dan tell me why will a sensible, educated wise old man zai kama ya aurowa matarshi yar aikinta? Nura yar aikina ka auromini sabida daidaicewa da wawatsula” uppan Nura baice mataba wardobe nata yabude yadauko kayanshi yawuce yafito daga dakin duk tana binshi yaje dakin Aman ya ijiye komi kan gado yafada bayin yayo wanka yafito yadauki cream din Aman yashafa still surfafa bala’i Hadiza take tsaf yagama yafito yasauka kitchen yaje yadauki babban kulan dake kan Island Hadiza takawo hannunta anan ne Nura yace “idan kikai kuskuren ko gigin taba abincin mahaifiyata Hadiza I will show inda haukanki ya tsaya anan nawa yafara” yana maganan yawuce ta yafita tabiyoshi tace “ai dama nasan kai mahaukaci ne dan mahaukaci kadai zai auroma matarshi yar aiki” fita yayi anan gaban kofa ta tsaya tana kallonshi dan bataso tafita tana fada, estate dinsu da ake ganinta as don aga tana fada, abincin ya ijiye a bayan mota ya kulle motan yadawo cikin gida Hadiza tasake binshi kitchen din yashiga ragowan friend Irish daya gani a pkate da egg yadauka, spoon yadauka yafito Hadiza nabiye dashi tace “ina zaka da abincin nan eh, Nuri ina zaka da abincin nan”? Dakin Ummi yabude yashiga biyoshi Hadiza tayi ciki ga mamakinta Nura just pushed her outside yamaida kofan yarufe yasa key tahau buga kofan da gudu tana ihu. “Nura ni kai pushing outside like that eh? Wlh wlh sainayi maganinka dakai da karuwan nan daka ijiye adaki” kallon Ummi yayi dayagani kwance kan gado kaman marainiya idanunta sunyi ja amman ba kuka takeba zama kusada ita yayi kan gadon yana ijiye abincin agefe murmushi Ummi tamai tace “shine saika kawomin abinci maisa kakemin aik…..” hannu yadaura akan bakinshi alamun tamai shiru hakan yasa tai shiru yakai hannunshi yadagata wajen window dakin yayi da ita ya yaye window yadaga wuyanta yana dubawa yana tattabawa ganin yadanyi ja yace “dazafi” dasauri ta girgizamai kai tace “ba zafi” yana kallon kwayan idanunta ahankali yace “mesa baki gudu ba dakikaga zata miki wani abu ko kiyi ihu ki kira sunana what it tamiki wani illan?” Murmushi tamai tacire hannunshi daga wuyanta tace “Anty bazata min wani illa ba ba muguwa bace, kawai fushi take sabida mun mata laifi” dan shiru Nura yayi yana kallonta saikuma ahankali yace “Ummi aure ba laifi bane like I said ranan nan ko nan gaba naji ina bukatan wata matan zan iya nakara aure, mata hudu zan iya aura” Ummi na kallonshi tace “Anty na sonka sosai, kuma soyayyan yasa take fushi haka” yana kallon kwayan idanunta yace “kefa?” Murmushi tamai tace “nima ina sonka sosan bala’i, tafashashen so ma nake maka my Noor bai huce ba” yana kallon bakinta yace “Allah yar matata”? Dan dariya tamai tace “da gaske, ba Hajiya zakakai asibiti ba lokacin na tafiya kazo kaje” dan ijiyan zuciya yasauke yace “banso na bar gidan nan ahaka” dasauri Ummi tace “babu abinda zai faru kaje ka kai Hajiya asibiti abincinta na kitchen a flask kadauka” ahankali yana kallonta yace “nadauka” ganin ya tsaya yana kallonta yasa tace “menene?” Yana kallon kwayan idanunta yace “Aman da Amal yaranki ne kada ki rabu dasu sabida Maman su kinji” murmushi tamai tace “tom Baban Aman da Amal” rungumeta yayi ahankali yace “kiyakuri da abubuwan da Hadiza tafada miki kinji, kada ki riketa azuciyanki, kiyakuri Hajiya Ummi” dudda taji wani iri amman tadaure tafita daga jikinshi dasauri tace “komi yawuce katafi” Gyadamata kai yayi yace “biyoni ki rufe kofan da key” biyoshi tayi yace “kiyi breakfast zan dawo yanzun nan” gyadamai kai tayi yabude kofa yafice tasa key dasauri ganin Hadizan na tsaye awajen yawuce Hadiza tasakebin Nuri tana masifa tace “tell this girl ko dakin yarana takara shiga wlh saina watsar da ita, karta kara taba wani abu that belongs to me in this house wucewa Nuri yayi yawuce yashiga motanshi yabar gidan Hadiza ta dawo sama tashiga surfafa zagi na uwa da uba ma Ummi, Ummi tayi shiru. Tashi Hadiza tayi ganin taki kulata tazo gaban dakin ta bubbuga tace “kifito mana idan ke diyar halas ce yadade da tsufa a inda yatafi yanzu, dagani saike agidan, kifito muyi magana woman to woman mace to mace, cus inada wasu abubuwa dazan fada miki kifito Ummi kibude kofan nan kifito” Hadiza tai dariyan keta tana tafiya tace “dan kauye dan kauye ne, ni wlh at this point ma tausayi kike bani Ummi, bari nafada miki wani sirri dabaki sani ba for free” tasake shiru tace “kinga Uwargidan miji itace kokon rayuwanshi, Ummi bar ganin kin zauna agidan nan kinga nida mijina munada yan matsaloli sai kikai yan dabarun ki na gidahuman kauye kikaja ra’ayinshi ya aureki to tsaya kiji wani abu dabaki sani ba game da mijina Nura” Hadiza takara murmushi tace “Nura kwata kwata dakikan mata dabasuyi boko ba basa burgeshi kije ki tambaya kiji, Baban Nura professor ne a BUK abinda yadawo dasu kano kenan daga zamfara, Hajiya wannan dakike gani tsohuwan secondary school English teacher ce, kannen Nura kap dukansu graduate ne dasuka gama jami’a har Meena Kwanan nan tagama bautan kasama, kinganni nan Nura bai yarda ya aureni ba saida nagama jami’a gabaki daya muna dawowa garin nan yasa nacigaba da karatun wuce jami’a wato masters sabida dan boko ne shi, yanason yaga matarshi yar gayu yar boko tanuna ma business partners nashi, kinsan mesa nake gayamiki maganganun nan”? Hadiza tasake dariya tace “sabida ke dakikiyace jaka kuma, Nuran dakike gani kin aura yau Nuran daya sami yar karaman matsala da Hadizan shice, kije kano ki tambaya abaki labarin kalan soyayyan damukayi, ban bashi jikina ba damuwa da sha’awa kinsan mutum shiru shiru mara magana yasa yaga kaman yana sonki wlh Ummi kindaiji na rantse miki Nura baya sonki sabida baki cikin kalan ko siffofin matan dayakeso” wani abu Ummi taji ya tsayamata awuya chak yaki wucewa takasa hadiyewa, Hadiza tace “bansan ko kinji magananmu jiyaba, jiya nace yasakeki zan chanza Ummi kinsan meyace mini”? Hadiza tai maganan cikeda tsantsan tunzura mutum saikuma ta kyalkyace da dariya tana tafi tace “wohoho ta yanda zaki gane kin tafka shirme Ummi kin auri mijina kin dauka kin sami gidan mijin cemin yayi nafara chanzawa tukunna yagani, idan na chanza nakoma Hadizata nada zai sakeki ki tafi mucigaba da rayuwanmu mukadai hankali kwance” dasauri Ummi ta tashi daga gadon zuciyanta na rawa tanajin wani iri, Hadiza tace “haka yadinga lallabani har saida ya samu nabashi hakkinshi that means keba komi bace awajenshi ba sati biyu dakukai kuna amarci kaman yanacin kashi haka yaji saida ya kwanta dani jiya yajishi daidai, yajishi damdam yajishi yakoshi, kuma kada ki manta rashin jituwan damuka samu dani da dashi yasa yaje yama nemeki” hawaye Ummi taji sun sauko daga idanunta, Hadiza tace “Ummi ki rubuta ki ijiye kwanan nan Nura zai sake ki kibar gidan nan dan bazai taba hada jini da jakan kauye ba da turenci nan nan bata iyaba wlh saiya sake k…….” Bude kofan Ummi tayi dasauri tafito idanunta sunyi jazur tahada idanu da Hadiza for the first time tunda tadawo gidan tace “Hadiza kinyi kadan ki rabani da Nura” sosai Hadiza ke kallonta ganin idanunta sunyi ja maganan ta shigeta kenan yasa ta taka zuwa gaban Ummi Ummi ta tsaya chak tana kallonta ba gudu ba jada baya, Hadiza namata wani kalan kallo tace “nabaki daganan zuwa sati biyu saikinbar gidan nan dan baki da waje awajen mijina” Ummi na kallonta tace “Hadiza ban auri Nura dan na kuntata miki ba, shiya nemeni da aure na aureshi kuma magana daya zuwa biyu zan fadamiki, nifa nayi miji kuma naga wajen zama, zama kuma daram! Wallahi ko ana hamaza hamata bazan rabu da mijina ba, barima kiji mutuwa kadaice zata iya fitar dani daga rayuwan Nura!” Hannu Hadiza ta daga zata kaima Ummi mari Ummi tarike hannun gam idanunta sunyi masifan ja kirjinta na tafarfasa itama jin ance Nura zai saketa tace “Hadiza kul!” Ummi tazare mata idanu kaman yar daba tace “dazu nariga nabarki kinmin hukunci sabida nasan ban kyautamiki ba na auri mijinki daya nemeni amman yanzu kikai kuskuren dukana Hadiza kin tuna kalan dukan da Meena tamiki”? Ummi tayi maganan tana kallon kwayan idanun Hadiza kaman yanda Hadiza ke kallonta mamaki yagama kasheta, Ummi tace “wlh saina miki dukan dayafi wanda Meena tamiki domin shiru shiru ba hauka bane, dan hakin daka raina shine yafi tsole ido, kul Hadiza! Wallahi kul! Duk abinda zakiyi kiyi but Ummi tariga tayi miji, kuma taga gidan miji, danhaka zama daram, dam, damm ehe! Sai kija please ki rungumi sorry dan haka askus me” ta yarda hannun Hadiza a air tawuce takoma dakinta tarufo kofa tasa key Hadiza tasaki baki mamaki ya cinyeta har zuwa bone marrow, she was like wattt! Ita village girl dinnan tama rashin kunya haka? Askus, askus? Did she just said excuse me as askus me? Sai kawai Hadiza tahau dariyan kuka, she’s laughing so hard and crying so hard as well, ita Nura zai auroma wannan jahilan askus me yar kauyen yarinyan???? Wow lugubrious!!!!! Mata Mata mata sau nawa nakira mu??? Please we should all learn to stop abusing opportunity sabida idan wasu suka sami that opportunity there’s nothing u can do in this world dazaisa su saki that golden opportunity daya shigo musu. That is what happened between Hadiza and Ummi, Allah yama Hadiza kyautan close to perfect husband but she abuse everything and toss him outside like a coin, Ummi grabbed that coin tace atafau koda za’a guntule hannunta ne she won’t let go off wannan coin din, wazakuyi blaming wacce tai tossing coin din ko wacce grab the coin??? Sainaji daga gareku and always remember shi opportunity sau daya yake zuwa miki. Allah ya kiyaye and see you’ll Saturday Fanmily and Askus me❤️ WEEKEND PROMO💃💃 I have special announcement masu son shiga class na MATAN AURE you can all pay 1k now kafin Monday yakoma 2k, registration is still ongoing kafin murufe. 🔊🔊🔊🔊🎊🎊🎊🎊🎊 Don’t miss MATAN AURE dina class for anything, I will give you all!! Sirri zan baku da dama Zan koya muku how to love mijinki in your own way kaman yanda Ummi keyi. Shagwaba, iya magana 🥰 Uwa uba iya kwanciya❤️, yanda ake siyan zuciyan miji, how to steal heart na Inlaws naki and so much more.😍 Idan kina tunanin asiri ko kayan mata ke siyan zuciyan miji come to my group na nuna miki gaskiya. HAUSA CLASS NE BA TURENCI BA REGISTRATION IS 1k NOW 6353995766 M Shakur world Moniepoint Send ur evidence of payment ta PC zanyi adding naki a group. click on this link and chat me up directly +2347012181461 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣4️⃣ Wai yan uwa yau magana ake ta kayan dadi da shan dadi, kun gane irin juice dinnan mai kaloli daban daban, kiga juice din kaman duka tattalin arzikin Nigeria ne aciki?? To ku tsaya kuji labari yau nakawo muku MOCTAILSBYTEEHA indai magana ake ta harkan Mocktails, milkshakes, frozen Mocktails and fresh juice 🥤 babu part two dinsu akap yanar gizo, zaki dan hada wata liyafa? Kirasu sumiki handling harkan abubuwan jika makoshi, for weddings, naming ceremonies, dinners, birthdays, graduations e.t.c name it zasu miki chat them up now ta hanyar clicking on this link👇🏼 karkuji tsoro service dinsu is affordable wa.me/+2348168045600 Idan kinason kiga hotunan kalolin juice dasukeyi da sauransu check them out a IG AND FOLLOW THEM❤️ Instagram handle @mocktailsbyteeha 14 Juyawa Hadiza tayi jin atmosphere na gidan has become so unbearable for her tawuce dakinta, gyale tadauko da wayanta tafito idanunta sunyi jazur kaman tayi wata daya tana kuka, kasa tasauka tadauki car key nata tawuce tabude kofa tafice ta shiga mota ko kallon gateman dinsu dake gaisheta batayiba tawuce ta tafi. Gudu kawai take shararawa akan titi, tayi nisa sosai ta gangara gefen hanya tai parking tadaga wayanta Anty Jamila takira tana bubbuga kirjinta dayake mata kaman an daura zuma rock akai, ringing biyu Anty Jamila tadaga duk karfin halin Hadiza kasa magana tayi, ita datagama cewa bazata kara kiran Anty Jams kan matsalolinta ba gashi yau tasake kira, kunya ma sai yasa takasa cewa komi kawai tahau kuka, shiruuuu Anty Jamila tayi tana jinta saikuma chan tace “gani nan cikin motan da mijinki yaturamin a airport za’a kawoni gidanki” dasauri Hadiza tace “eh”? Dan batagane tana hanyar zuwa gidan ta ba, dan jim Anty Jams tayi tace “mijinki dake bala’in sonki dakin kasa gani cus you’ve gone blind, dakanshi yakirani tareda Baban su Waleeda yarokeshi da cewa you need me right now nazo abuja, dakanshi yamin booking flight to and fro, yaturamin ticket ta WhatsApp, gobe zan koma kano dasafe, gani a mota, yanzu dai kina ina dan naji karan motoci”? Cikin kuka Hadiza tadago kanta bamatasan inda takeba hakan yasa tace “kizo shagona” katse wayan tayi Hadiza tasake tada mota taja kusan atare daga ita har jams sukakai shagonta, Babba ce Anty Jamila dan akalla zatakai 42yrs itace first born dinsu, Hadiza na ganin yayarta bata damu da suna plaza ba da gudu tai wajen kawai ta rungume Yayanta bakaramin tausayinta Anty Jamila tajiba, duktai zuru zuru, idanunta sun kumbure, fuskanta duk yakoma ja sabida kuka gashi yau kodan makeup da gayun data saba batayiba sabida damuwa, dagota Anty Jams tayi tace “ja gyalenki kirufe fuskanki muje ciki” yanda yayarta tafadi haka tayi suka shiga cikin babban shagonta staff din Hadiza na gaidasu Anty Jamila ce ta amsa suka wuce sama Hadiza tabude office nata suka shiga tana maida kofan tarufe sai kawai tayi wajen Anty Jamila data sami waje kan kujera tazauna. Zama Hadiza tayi dirshan akasa takifa kanta akan cinyan Anty Jamila sai kawai tahau kuka. “Anty Jams na shiga uku, wlh na shiga uku na lalace, Nura ya cuceni, ya ci amanata ya yaudareni, Nura ya cuceni yakuma wulakantani” dudda yanda kanwar tata tabata tausayi but Hadiza needs to hear the bitter truth, da dan zafi Anty Jams tace “wlhy Hadiza kene kika cuci kanki, kika wulakanta kanki, kika yaudari kanki, u did all of this to yourself” Dasauri Hadiza takalli yayarta takai hannu tana share fuskanta tace “Anty Jams is it a crime kanada yar aiki? Laifi ne daukan yar aiki? Yarda danayi nakuma aminta da mijina cus zanma Nuri shaidan nan har ranan gobe kiyama shi ba dan iska bane kuma ba manemin mata bane, hasalima irin mazan nanne da mata basu damesu ba, Anty jams kiduba kiga this big shago i mange everything dakaina, am a business woman, an entrepreneur da aka san dani, I need to maintain level na integrity da face na business dina, niba housewife bace and I have kids so dole na dauko yar aiki dazata dinga managing mini gida da yarana, but shine Nuri zaibi bayana ya auremini yar aiki? Kinsan yanda nakeji azuciyana kuwa? Yar aiki ta fa? Yarinyar dana dauka tanamin bauta zai auro mini, Anty Jams jinake kaman na mutu kawai nahuta yafimin, naji na tsani kaina nagaji ma dakomi” takara kai hannunta ta share hawayen dasuka zubo mata saikuma takama bakin gyalenta tadaura kan idanunta, sosai Anty Jamila ke kallonta yanda Hadiza is looking this humble, ta zauna dabas akasa gabanta kaman mai daukan karatu tana kuka yasa saitaji kaman itama ta tayata kukan but dole ita ta daure, mikewa tayi zuwa table tadauko kwalin tissue tazo wajen tazaro daya ahankali takai kan fuskan Hadiza tashaga sharemata hawayen cikin fada irin ta manya tana goge mata fuskan tace “kinga abinda I’ve been telling you ko all this while but kikai kunnen uwar shegu dani, Hadiza kalli yau yanda kike kuka wiwi kaman bakeba, Allah yasa hakan yazama darasi agareki Hadiza, Allah kuma ya shiryeki ya ganar dake gaskiya yacire miki bakin akidan nan dakika dauka kika daurama kanki dayay landing naki in this situation, Hadiza ina ganin nafiki jin bakin ciki da Nura yakirani dakanshi dazun dasafe nida Baban Batool yana fadamana gashi gashi yayi aure, Ya aure Ummi and u don’t look okay plssss Baban Batool yabanni nazo naganki just for today gobe nakoma” Anty Jams taidan shiru tareda ijiye tissue daya gama jikewa tanunama Hadiza dake kallonta da jajayen idanu kirjinta tace “I was deeply hurt wlh danaji maganan but then again koda murya zan chanzawa Nura wanda zai nuna labarin baimin dadi ba nima nazama butulu kaman ki dan nasan kanwata ce caused everything and Nura has been annoyingly patient dake, cus hakurinshi ma at a point haushi yake bani yanda baitaba daddaura miki mari ba yafasa miki bakin dakikemai rashin kunya sannan yakado ki gida” Anty Jams tayi shiru tana kallon yanda Hadiza ke silent kuka tana shesheka tace “babu the most bitter punishment da zakama matarka irin ka auromata yar aikin ta, Hadiza yar aikin ki fa dababu abinda bata saniba dake faruwa agidanki ba, yarinyar dake zama cikin gidanki safe, rana , yamma, dare dakuma another safiya har na tsawon close to a year, rana daya mijinki ya aurota a matsayin kishiya Ya Allah! Allahumma Ajirni fi musabati!” Saikawai Hadiza tarushe da kuka Anty Jams ta girgizakai tace “I was deeply hurt but I couldn’t say a word sabida kin riga kin sani a position din dabazan ma iya bude baki nacema Nura haba Nura maisa zakawa Hadiza wannan sakkayan, but nakasa dan Hadiza ni kaina wani zubin idan kikai wani abun jinake kaman kada na sake kiranki har abada but then again bazan iyaba jini yariga yayi bounding dina dake for life, ni kenan balle kuma Nura dashine kikafi yima kashi aka, atleast ni kinadan shakka na kina ragamin, but still last time damukai magana cewa kikayi bazaki kara kirana ki gayamin matsalanki ba cus blaming naki nake now have u seen abinda nake fadamiki?” Hannu Hadiza tasa tajawo tissue tadaura kan idanunta Anty Jams tace “bangaya miki halin dakikema Nura zai iya pushing nashi waje ba? Ban gayamiki ba”? Gyadama Anty Jams kai tayi tana goge kwalla, shiru Anty Jams tayi tana kallonta tace “kinason mijinki amman haukanki yasa aurenki gabaki daya is shaking Hadiza, look at abinda kikama kanki, look, Nura ya auro miki mai miki aiki, wani cin zarafi yakai haka have u seen inda I know my right, nida mijina are equal, feminism, rayuwan Abuja, bla, bla, bla yayi landing naki? Kinga result din yanzu? Have you seen the outcome”? Anty Jams tayi maganan da fada sounding so pained irin fadan babban yaya da karaman kanwarta dinnan, yanda Hadiza kema yayarta kuka yasa itama Anty Jams taja tissue tadaura kan idanunta dan takasa rike hawayen cikin kuka tone tace “kin kashe kanki abanza a wofi da bakin halin dakika samo Hadiza, miji mai kirki, mai hali irin Nura, gidanmu babu wanda Nura bai taimaka ba, Mama idan tai rashin lafiya kudin dayake turowa harsai na mai fada, yamana renovating gida, nan nan saida yayi shiga yayi fita yasaman ma Babban Batool contract na titin nan akano, eh? Kinada mijin arziki, mijin kwarai mai hankali, mara mako, hannun Nura abude yake koda yaushe, gashi yana sonki, wani zubin nakance Badadan nasan baki harkan malamai ba danace mallakeshi kikayi tsabagen yanda yake sonki, kimai wulakanci da cin mutuncin duniya but still yana tareda ke, har uwarshi kika daukoma dan sanda ranan ne yafara sakinki wanda shima washe gari yadawo dake maza nawa ne zasu iya haka? Wani kika zagi mahaifiyarsa ko kije extend na daukoma familysa police that’s the end of the Marraige koda jikin gwal gareki kuwa, but still Nura yacigaba da zama dake and u still won, cus ai kince bazasu zauna agidan ba kuma basu zaunan ba sun barmiki gidan, so akanmene yanzu idan yakirani yacemini yayi aure ya auri yar aikin ki zan iya cewa wani abu bayan nasan abinda kanwata tayi iyye? Waye aduniyan nan zaiji abubuwan dakikama Nura bazaiyi supporting kishiyan dayamiki da yar aikin ki ba eh? Hadiza bakanki kadai kika cutaba har mu nan gabaki daya kika cutar” kawai Anty Jams tahau kuka dan abin namata zafi arai cikinsu babu mai lallashin wani. Da kyar Anty Jams tayi shiru takalli Hadiza dake kuka har lokacin tace “bawai baki nake miki ba but ace yau Nura yarabu dake wlh harki mutu Hadiza bazaki kara samin miji kaman shi ba, kuma idan zakiyi aure dari haka za’a dinga sakoki cus bakene matsalan ba halinki konace sabon halinki ne matsalan, namiji da mace ba daya bane, a man and a woman are not equal stop believing in that stupid theory! A house belongs to a man, gidanshi ne, shiya auroki shiya saki aciki, bakida right or whatsoever kice saida permission naki baki zasu shigo Hadiza, dafa abinci is traditional da globally mata aka barma wannan tradition na girki agida, tundaga upbringing ba’ayin rainon maza to be entering kitchen mata akema wannan training din so akanme zakice shiya shiga kitchen? Ya iya girkin ne? Kula da yara aikin mace ne idan mijinki yatayaki is fine idan baitayaki ba kada kice dole saiyayi dan shine ke fita kullum cikin rana yaje yanemo muku abinda dagake har yaran zasuci, Hadiza dan mijinki yace tashi bani kaza, yimin kaza, zonan, zauna, matsa, baya nufin ya rainaki bane No ya isa ne saisa yabaki umarnin kuma dole kibi, idan bazaki iyabiba idan u can’t subject kanki to follow umarnin mijinki maisa kika aureshi to??? Eh” cikin kuka Hadiza tace “wlh Anty Jams zan chanza nagayamai zan chanza amman yasaki Ummi mucigaba da rayuwan mu mukadai” dan murmushi Anty Jams tayi tace “Hadiza kenan u can’t eat your cake and still have it! Yanzu ace Nura yashigo nan kifadamai maganan nan agaban idanunki zance Nura kada ka saki Ummi” Hadiza nawani kalan kallon Anty Jams tana kuka mai tauna zuciya, Anty Jams tace “Hadiza a rayuwa one cannot always win, tunda kikai aure yau shekara goma going to 11 you’ve been winning akomi nakeda Nura, yanda kikeso haka ke faruwa agidan ki, kika fitini bawan Allah he let u have it ur way, wannan ma ishara ce Allah ya gwada miki dan trust me, Allah ne ya kwadaita ma Nura son ya auri yarinyar nan Nura da bayama kallon mata, rana daya yaga Ummi yaje har kauyensu ya aurota, inaso nagaya miki is too late for you amman I can’t because is not too late for you” Anty Jams tadanyi shiru tace “is too late for you cus Nura yariga ya auri Yarinyar nan ba gudu ba jadabaya, so kike yakoma karamin mutum ya auri yarinya sabida ke da bakimai biyayya ba yasaketa angayamiki batada iyayene? Wasu iyayene zasuso su aurar da Yarinyar su asakota bayan kwana biyu so maganan Nura yasaki Ummi ki manta dashi kawai” taushe bakinta Hadiza tayi dan ihu ne yakeso ya kufcema bakinta, ijiyan zuciya Anty Jamila tasauke tace “abinda nake Nufi is not too late for you shine Nura har yanzu yana sonki sosai, cus namijin dake tsananin sonka ne zaiga halin dakake ciki yabukaci wata yar uwanka tazo just for your comfort, Hadiza har yanzu Kece keda ragaman zuciyan Nura forget ya auro wata Ummi koda tanada wani abu axuciyanshi to akalan zuciyan ne, bazaka iyajan akala abu ya motsa ba amman mai ragama shine keda ikon komi, so Hadiza idan zaki gyara halinki from today ki koma asalin Hadiza da Nura falls for deeply lokacin nan kowa yasan labarin soyayyan ku a kano ki koma i assure u, u will come me to tell me wonders, is not too late for you Hadiza” Hadiza na kuka tace “to mezanyi? Yanzu haka zan zauna yadinga yanda yaga dama dani?” Yayarta na kallon kwayar idanunta tace “kwarai idanma takaki zaiyi yayi ke har kinada baki mutumin daya miki komi, the journey might be tough on you but inhar kika dage mijinki nakine Hadiza” sosai take kallon yayarta, ahankali tanuna zuciyanta tace “anty Jams inaso na tsani Nura so bad sabida auromin Ummin nan dayayi amman nakasa sai kace yamin asiri yanzu nema naji wani kalan sabuwar soyayyanshi nakamani danaga ya auro wata ina masifan jin zafi da kunci ko dakinta da dazu yashiga agabana wlh kaman ana yankani alive mesa nakeji haka? Maisa nakasa fushi namabar shi da yar aikin gabaki daya afterall bana bukatanshi inada kudina dazan iya kula da kaina aduniya, why why why maisa yanzu ne nakejin sabon soyayyanshi araina da inji na tsaneshi?” Anty Jams tace “sabida yanzu ne kikasan menene kikai loosing kokuma nace menene kika bari ya kufcemiki a hannu, all this while ai ina fadamiki kina mugun son mijinki amman kaman bake nake fadamawa ba sai yanzu dayay aure kikejin kina sonshi kawai da hankalinki da karatun ki kin cuci kanki abanza a wofi Hadiza, Hadiza Allah yabaki perfect husband, kinsan maza nawa kenan aduniyan nan da basa ciyar da matayensu sabida sunga matan na sana’a? Kinsan maza nawa ke bama matansu 200 kullum kudin cefane and matan su karba and fix something with it? Kinsan mata nawane da sunma manta when was d last time mazajensu suka musu dinki tun na akwati? Hadiza kinsan maza nawane a zamanin nan da bama su damu da yaran cikinsu da suka haifaba sun barma matayensu yaran sune cinsu, shansu, suturansu harma school feees nasu mazan na nan kuma bawai sun rasa kudin biya bane, Hadiza kinsan mata nawane yanzu that are going through domestic violence, bullying, torture damuwa da rashin sukuni agidan mazajensu from both mijin da yan uwan shi? And all this matan despite everything suna zaune agidan mazajensu despite ba sabulun wanki bana wanka, ba kudin kitso ba kudin kayan salla but ke kinsami everything, banda doraki dayayi akan business yasan kinada kudi baitaba kallon kudinki ba, for once baitaba cewa kuyi sharing bill ba, baitaba kin sayo wani abu ba, yan uwanshi ko mahaifiyarshi basu taba takura mikiba saina girmamawan Matan yayansu dasuke miki not until ranan da kika zagi mahaifiyarsu agaban Meena ta dauki action which I support dan banabin karya, kinsan mata nawa ke neman wannan jindadin dakika samu agidan mijinki? Kinsan how many women out there are dying to be in this position u are?Hadiza jibi rahama da baiwa daban daban da Allah yamiki, which of the favors of Allah can you deny??”Hadiza tai shiru tana goge idanu, Anty Jams tace “all abinda Nura ever wanted from you is just care, care for him care for his kids, attend to him and attend to his kids yataba demanding for more than this?” Girgizamata kai Hadiza tayi tana kuka komi nadawo mata fresh tundaga farko rayuwansu, ijiyan zuciya Anty Jams ta sauke tace “like I said is not too late for you cus Nura namiki wani special so azuciyanshi maybe sabida kene first love dinshi dan haka maza maza ki gyara before u lost him for good kısan inda dare tamiki and I will tell you this again kishiya fa yarıga yamiki, kidauki hakan amatsayin kaddara dakuma hukunci da Allah yamiki abisa laifinki Hadiza ki tuba taubatan nasuha kikuma chanza inba hakaba kindaisan haka nake gaya miki gaskiya baki yarda saiya kwabe miki, inba hakaba Hadiza wlh wlh zaki rasa Nura for life” dasauri Hadiza takalli Anty Jams idanunta sun nuna asalin fear gabanta nafaduwa, Anty Jams tace “kuma ki kara rubutawa ki ijiye again bazaki taba samun mijin dazaici kashinki kaman yanda Nura yaciba, idan zakiyi aure sau 1000 zaki fito so 1000 cus akidarki dabi’unki ne matsalan, beauty bashi ke keeping aure ba, being classy bashi ke keeping husband ba, having money ko business ko wayewa bashi ke keeping mijiba u of all people can tell people this yau bagashi Nura ya auro miki wacce batai makaranta ba, yar asalin kaune, Hadiza abinda namiji keso shine yasami mace dazatamai abinda yakeso which bakiyiba” daura hannunta Hadiza tayi akan idanunta sai kawai tahau wani kuka kai Anty Jams bata tabajin Hadiza tabata kalan tausayin data batayau ba tunda suka girma, ahankali tace “zonan Hadiza, come here” jawo Hadizan tayi tadaura kanta kan cinyanta tashiga shafa kanta ahankali tace “kidena kuka haka, ya isa ki yarda da kaddaran ki we all are humans, and yin mistakes yana kara tabbatar da yes mu fa yan adam ne we are bound to make mistakes, but what makes us special and unique is wannan ability na gyara mistake naka, trust me Hadiza is not too late u can amend all the broken relationships starting from Nura, apologize and become the good wife daya dade yana kwadayi yagani awajenki and zakiga Nuran ki zai dawo miki A man is like a little baby idan kika lallasheshi yana lallasuwa, yaranki ki karbesu, kin dauki cikin yaran nan for nine whole months, kika haifosu bar ganin baki gabansu as far as jininki ne su wlh wlh babu wanda ya isa ya chanza haka all it takes is kawai kijasu jikinsu, hug them that duminki dasuka dade basuji ba let them feel it, take them with u to kitchen cook for them and feed them da hannunki, bath them take them out to any park suje suyi wasa spend quality time da yaranki Hadiza and see idan sun kara kallon Ummi and last but not least Hajiya!” Anty Jams tadanyi shiru sanman tace “kinma Hajiya Babban laifi ta hanyar zaginta dakikayi da dauko musu police but Hajiyan dana sani is just like Nura, she’s a wise woman data haifi yara mata da yawa she knows how brain namu operate, she’s a mother trust me kikaje kika bata hakuri koda ta wayane wallahi she will forgive you and life goes on, Hadiza respect is earned baka demanding dinshi by fire by force, idan kika kama kanki kika sauke all duties naki as a wife wallahi Nura babu abinda bazai miki ba the, forget al’adun yan garin nan bakiji karin maganan nan ba idan wani yazo kasuwa yayi rawa yasami kudi wani yazo yayi duka zaici and this is exactly abinda yafaru dake, akidan wasu dakika dauka dakikaga works for them ke yajamiki saki dakuma kishiya, Hadiza u are educated I believe the only wanda ya chanchanci kayı pleasing aduniyan nan is Allah bawani ba ki manta da kawayenki and be you and win ur husband kinji” Gyadamata kai Hadiza tayi ahankali, Anty Jams tace “as for Ummi kada ki sake ki bata hurimin ta rainaki ki kama kanki babu abinda ya shafeki da ita ko harkanki trust me idan kikai haka bata isa tamiki maganan banza ba ke koma tayi gigin yi Nura zai taka mata burki I trust him kinji Hadiza” Gyadamata kai tayi, Anty Jams na shafa kanta tace “nasan da ciwo but kikai zuciyanki nesa and amend your path okay “ sake Gyadamata kai Hadiza tayi, sosai Anty Jams ke shafa mata kai tun tanajin sheshekan kukanta har wani baccin damuwa yayi awon gaba da ita ahaka. ** Kusan awanshi daya da rabi da fita Ummi tayi dialing number shi, wayan na gab da katsewa ya daga yace “Hajiya Ummi” har cikin ranta Ummi taji yanda yakirata sai zuciyanta ya narke tana kara addu’a Allah karyabawa Hadiza ikon rabata da mijinta, cikeda danne damuwanta tace “dama nakira naji yaya kunkai asibitin ya jikin Hajiya kuma?” Dan shiru Nura yayi wallahi bazai iya kwatanta yanda this small small things da Ummi keyi counts in his heart ba, this has been abinda he desperately wants Hadiza tamai, murmushi yamata yace “eh munkai asibiti, jikinta kuma dasauki tagama ganin Dr dake managing ciwon suganta yanzu tana ganin likitan dake managing hawan jininta” ijiyan zuciya Ummi tasauke in a very caring way tace “amman akwai cigaba sosai ko?” Cikeda tsananin jin dadi yace “akwai Allhamdulillah” ahankali Ummi tace “naji dadi, Allah yabata lafiya gabaki daya ta warke tass tass” wannan karan murmushin dayayi saida Ummi taji yace “Ameen thank you Matata” yanaso ya tambayeta ko Hadiza ta dameta but baiso yabata room to think ill of Hadiza hakan yasa yace “kinci abincin dana kawomiki”? Dasauri tace “eh nacinye tass sabida abinci yayi dadi sosai” ahankali yace “ai kin iya girki saisa” cikeda so Ummi tace “a’a bahaka bane sabida kaika kawomin abincin saisa yakara dadi Allah kuwan” murmushi yayi ya jingina da mota tareda lumshe idanu ahankali yace “nayi kewanki sosai Ummi kaman nayi shekara bana taredake haka nakeji” lumshe idanu tayi ahankali tace “jiya gabaki daya nakasa baccin kirki, duk inda najuya bayamin dadi kaman ina kan icce nasaba da jikinka” cikeda so yace “gobe in sha Allah muna tare kinji Abu” dan dariya tayi ashagwabe tace “ni banson ana kirana Abu” dan hade kafanshi yayi dasauri yace “to to naji nadaina tuba nake” murmushi tayi saikuma murya chan ciki tace “I lobe you my Noor” lumshe idanu yayi wannan karan saida yakai hannunshi yadaura kan gabanshi dayaji ya harba, cikin wata kwantacciyan murya yace “kinaso nabar Hajiya nagudo gidane”? Shiru Ummi tayi itama tana lumshe ido wlh 2days dinnan kaman shekara mugun kewanshi dakuma sha’awanshi takeji kasa magana tayi ta girgizamai kai alamun aa, murya chan ciki Nura yace “I love you Hajiya Ummi na” murmushi tayi tana kokarin kauda maganan jin muryanshi yayi sanyi gashi yana asibiti tace “uhmmmmm” anatse paying close attention to her yace “menene da wani abu ne”? Cikin kwantacciyan murya tace “ahmmm dama inaso namaka magana ne kan Hajiya tadawo nan umm” tadanyi shiru saikuma dasauri tace “kaga gamu mubiyu anan ba dadi Hajiya na wani gidan daban zaune, koda Baffan baice komiba but abin zaiyi kaman bamujin maganan ka, dan Allah kadawo da Hajiya nan gida namaka alkawari zamu kula da ita da kyau” Shiru yayi kawai, yadade bai hadu da yarinya mai wayau kaman Ummi ba gabaki dayan statement nata bata aibanta Hadiza ba rather maganan tayi as per subiyu atare zasu kula da Hajiya tama Hadiza kara dudda tasan Hadiza baza tayi ba, kuma gaskiyanta ne it looks somehow matanshi har biyu amman mahaifiyarshi na zaune a gidan Baffan shi koda basuce komiba is somehow but Hajiya yake tunani da kyar inta yarda yarıga yamata maganan tanuna a’a, dan ijiyan zuciya yasauke yace “Hajiya bazata yarda tadawo ba Ummi” dasauri Ummi tace “kabani izini nakira Hajiya dakaina na mata maganan”? Batare daya musa ba yace “eh ki kira muji” murmushi Ummi tayi tace “nagode Baban Amanu” ahankali Nura yace “nagode nima Maman Amanu Hajiya taji dadin tuwon dakika mata duka gidan har Baffa da ni shi mukayi kari dashi, Matan Baffa na tace nagaya miki keda itane kinsa abincin data dafa yayi kwantai” dariya Ummi tayi tace “ahh ah ahh nayi babban laifi, katayani bada hakuri kuwa”? Dariya yayi yace “ni ina ruwana” kaman zata rushe da kuka tace “kai dan Allah Baban Amali” dariya sosai Nura yayi harya manta damuwan Hadiza daya addabi zuciyanshi yace “nabada wasa nake miki” murmushi tayi tace “godiya nake ka koma wajen Hajiya ka gaidamin da ita kaji saika dawo” Gyadamata kai yayi yace “in sha Allah” ya katse wayan feeling so happy. Ummi na gama wayan wani kira yashigo wayanta dasauri ta kalli wayan number ne but ba irin na Nigeria ba bata saba ganin kalan number ba dauka tayi kafin tayi sallama taji muryan wata mace dayadan manyanta ba chanchan ba. “Ummi, Aisha ce, kanwar Ya Nura dake Egypt” dasauri Ummi tazaro idanu ganewa datayı itane maibin Nura cikeda kunya da bala’in girmamawa tace “laaa Ya Aisha ina yini, ya aiki ya yara da Babansu” murmushi Aisha tayi tace “Alhamdulillah Ummi, musamman nakira wlh Hajiya tasanar dani yanda kike dawainiya da ita, tace yau kene kika aikomata da karin kumallo sannu da kokari Ummi angode angode, ina zuwa dan Allah dakata kadan nakira Asma’u da Rukayya muyi conference call suma sunaso daman su kiraki” kafin Ummi tayi magana harta shiga kira nan da nan sukahau conference call sai godema Ummi sukeyi akunyace Ummi tace “dan Allah kudaina godemin haka, Hajiya mahaifiyata ce banga dalilin godiya dan nama mahaifiyata abuba, nima sonake nasami albarkan dakuke samu, bantaba sanın zan sami wacce zata maye gurbin mahaifiyata aduniyan nan ba bayan tarasu sai Hajiya, Hajiya Itace mutum nafarko tunda nafara aaikatau dudda tana mahaifiyar mai gida bata kyamaceni kaman yanda akeyi agarin nan ba takirani tasa na sauna mukaci abinci tare sannan tasaka Meena ta tayani aiki, itane mutum na farko da bata tabamin kallon yar aiki ba sai diyarta kuma tabani tukuicin girki da babu sanda yataba bani, Hajiya dabance araina kudenamin godiya kan wani abu ban mata komiba Mamana dana rasa Allah yabani a Hajiya” tai maganan muryanta nadan rawa yau ta tuna da mahaifiyarta kannin Nura jisukayi sun kamu da son Ummi atare sukace “kidaina kuka Ummi Allah ya Jikan iyayenki da rahama” ahankali tace “Ameen nagode” saikuma suka shiga hira tana tambayan su sunayen yaransu, yaran Aisha Hudu, Yaran Asma’u biyu, yaron Rukayya daya Ummi harda magana da yaran tana wasa dasu yaran najin dadi kusan 30min suna hira kaman sun saba, suna shirin sallama Ummi tace “Ya Aisha, Ya Asma’u and Ya Ruky dan Allah ku tsaya inaso nayi wata yar magana daku” dasauri giving her full attention sukace “okay Ummi muna jinki” anatse Ummi tace “dama inaso Hajiya tadawo nan nayi magana da Baban Amali yace Hajiya bazata yardaba saidai ni nayi to inaso anjima suka koma gıda zan kirata dakaina, amman dan Allah inaso kudan tayani sa baki ku lallaba Hajiya ta yarda tadawo nan zamu kula da ita wlh baza’a samu mata sala ba” kamin Ya Aisha tai magana Asma’u tace “Ummi kinga basaikin kare Hadiza ba kinga idan Hajiya tadawo gidan nan Hadiza ta kara zagin mini uwa wlh zanbar nan Port harcourt ne nazo harnan Abuja na nuna mata idan batada tarbiya zan bata sabo” dasauri Ruky tace “Meena kadai ta isheta ai basai munzo ba, amman nima nafison Hajiya na nan gidan Ya Nura da gidan Baffan mu gaskiya dudda Matan Baffa batada matsala but Ya Aisha me kikace?” Anatse Aisha tace “bari zan kira Hajiya namata magana but Meena tagayamin Hadiza bata sonsu agidan ne Ummi Hajiya nada hawan jini banso tana ganin tashin hankali kwata kwata” dasauri Ummi tace “laa wlh Anty bahaka takeba, lokacin nan kaman tanada dan matsala ne saisa hakan yafaru amman Anty nada kirki kuma tana kaunar Hajiya ba kadan ba, kada ku damu zamu kula da ita sosai wlh” murmushi Aisha tayi badan komiba saidan yanda taga hankali da dabaru irin na mata na Ummi dudda tasan Hadiza bawai chanxawa tayi ba but for the sake of Ummi dakeson Hajiya tadawo gidan harma she’s putting it in request yasa tace “shikenan Ummi zan ma Hajiya magana” cikeda farinciki Ummi tace “yauwaaa nagode sosai Ya Aishan muuu” su Rukayyah duk dariya sukayi Aisha tace “menene tsawon dogon riganki Ummi”? Ahankali Ummi tace “hamsin da takwas” cikeda so tace “zan saya miki dogayen riguna na aiko miki ta airport sai Ya Nura ya karbo miki” cikeda murna Ummi tace “Ya Aisha nagode nagode Allah yabiyaki yama yaranki Albarka” duk dariya sisters din sukayi cikeda son Ummi ganin Nura ya auri mata mai hankali yanzu sukai sallama suka katse Ummi sai dadi takeji. Sun gama komi a asibiti suna hanyan komawa gida Aisha da kannenta suka kira Hajiya a conference call, Nura yana jinsu suna cewa Ummi ta aikosu cus wayan Hajiya is always on speaking suna lallaba Hajiya takoma gidan Nura, Nura sai mamaki yake shi baimasan Ummi nada number kanninshi ba dudda dai Hajiya bata yardaba cemusu ma tayi su daina damunta suna kaiwa gıda ta zauna adakinta Meena takawo mata ruwa saiga kiran Ummi wayan Hajiya tadauka tanunama Nura dake gefenta yana danna waya tace “wato yaran nan nan hada baki sukai” wayan ta dauka kafin tayi magana Ummi tace “Hajiya ina yini, ya karfin jiki kun dawo”? Hajiya na murmushi tace “lafiya lau Ummi jiki kuma Alhamdulillah nasami lafiya sosai an bani magani na sati daya daganan nakoma likita ya ganni sai kano in sha Allah” ahankali cikeda rage murya Ummi tace “Hajiya dudda ance Anty na fushi dani yau amman muna kishin ladan ki da addu’anki datake samu ita kadai kullum, Hajiya dan Allah kidawo gidanki muma musami ladan nan da addu’anki kinji Hajiyanmu” Wlh Nura tunda yake baitabajin wani sabon soyayya da respect na Ummi dake shiga zuciyanshi irin na yau ba, just look at yanda tai putting maganan mind blowing! Ita kanta Hajiya jitayi kanta yayi girma saita kama baki tace “auuu hakane bari Karime tajiki keda itane” dan dariya Ummi tayi adan shagwabe tace “Hajiya dan Allah kidawo kinji har Auta Meena bazan bari tana damunki ba” Meena dake wajen tana murmushi tace “inajinki” dariya Ummi tayi tace “Meena please tayani lallaba Mamana tadawo gıdanta kinji” harga Allah ita kanta Hajiya tafison gidan danta da nan ba yanda ta iyane batason taxama silan haddasa fıtina agidan danta saisa tadawo nan din, ahankali takalli Nura daya lumshe idanu kaman baya jinsu Meena tace “Hajiya please mu koma chan kinji bahayaniya agidan Ya Nura kaman nan” dasauri Ummi dakejin komi tace “Hajiya dan Allah kidawo kinji babu wanda zai tadamiki da hankali ko damunki sabida ke Anty har shopping tafita yi yanzun nan ma” Sosai Nura ke mamakin Ummi, murmushi irin na manya Hajiya tayi tace “tunda dai kun taru kunmin chaaa aka hardasu Aisha kike aikomin sabida nacema mijin naki a’a dayamin magana ai shikenan, anfi karfina anmin taron dangi, gobe da safe nadawo koda rana in Allah yakaimu” daga Ummi har Meena dake wajen ihu sukayi Nura yadago yakalli Meena dasauri ta taushe bakinta cikeda farin ciki tana dan dariya, Ummi tace “Wayyoo dadi Mamana zata dawo gida gobe, mezan dafa miki eh Hajiya na gobe” har cikin zuciyanta Hajiya kejin dadin yanda Ummi ke nan-nan da ita ahankali tace “kome kika dafamin zanci Ummi Allah yamiki albarka, Allah ya farantamiki kema, Allah yakara daidaita zamanku dake da Hadiza, nagode ko Ummi” cikeda murna Ummi tace “Ameen Hajiya kinga harmun fara samun albarkanki tun yanzu” dariya Hajiya tayi sosan gaske irin na manya tace “Allah kara miki Albaraka to” kyalkyacewa Ummi tayi awaya tana dariya tana Ameen shima Nura yayi dariya sosai feeling so happy and satisfied a zuciyanshi yace “Ameen” he’s really happy with the way Ummi made his mom felt just now, from voice din Hajiya kadai she’s feeling soo pleased and special Alhamdulillah for the first time tunda yayi aure matanshi made his Mom his happy, just look at yanda Ummi tayi magana ki dawo GIDANKI!!! Murmushi yayi sai kawai yaciro wayanshi he don’t care ko zata gane ko bazata gane ba dudda yasan ta iya karatu but he just typed. “I love you Ummi na” yamata sending❤️. Like I said duk zafin challenge da kika facing agidan aurenki there’s always a simple solution to it, all it takes is the willingness and zeal naki gyara but kuna ganin Hadiza zata iya gyarawa??? Nura kam na son Hadiza so ma ba kadan ba, mutum da zaije to the extend yabiyama sister ki ticket just to come and be there for you ai karshe ne, kuna ganin zata iya bawa Nura that love, care and affection dayake nema awajenta kuwa ido rufe??? My question still stand can Hadiza change kuna ganin zata iya?? Now bari mu leka Ummimyn kauye. Kunsan akwai ilimi that’s knowledge sannan kuma akwai Wisdom shine hikima ko a hausance? Rayuwanmu ayau akwai mutane dayawa masu ilimi but basu da wisdom if u ask me zan iya cewa Hadiza is one, she’s educated but she lacks wisdom, bata iya siyasa da kirsa da kisisina da iya siyan mutane ba, zero pretending and kara, batason abu tanuna maka karara. Believe me idan nace Ummi might be uneducated but yarinyar tanada wisdom and I will give it for Gwaggon ta zama da tsofaffi nakoyamaka dabarun zaman duniya da dama. Now akwai wani magana da iyayenmu keyi akace “idan ka auri miji ka auri all the family” yanzu kuna ganin misali nan gaba idan Nura yayi kokarin sakin Ummi kanninshi da mahaifiyarshi zasu yarda yasaketa?? Aganin ku maisa bazasu bari ba? The logic is simple always pick on this small small abubuwan and keys danake samuku a novel din nan, ina kawo muku bangaren both Ummi da Hadiza sabida masu ilimi susan sunada chance arayuwa, marasa ilimin kimiyya suma susan sunada chance arayuwa to attain success all it takes is iya xama da mutane, magana mai dadi, nabarku lafiya yan uwana makaranta littafin nan makesure kun shiga class dina danakeyi na matan aure with just 2k you can bring your wife, sister, cousin, friend koma waye dakukaga tana bukatan karatuna, idan kinason magana dani M Shakur kuma chat me up a whatsapp wa.me/+2347012181461 Zaku iya samuna kuma a Instagram @mshakur_world hakama a TikTok mshakurworld. I see the love dakukema this book and inada gagarumin albishir dazan muku gobe in Allah yakaimu, Thank you and Godbless❤️ 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣5️⃣ Kun tuna albishir din danace zan muku yau???🥰 Here we go, MATAN KO MAZAN chapter 1 is coming to an end just few more episodes to go which nakega zan gama mukushi within this week now here comes the EXOTIC NEWS konace the most EXCITING PART of the news shine Chapter II namu wanda is about CHEATING!!!! Did you know acikin kaso dari na ma’aurata 90% na cheating?? Ko kiga mijin yanada babes awaje ko kiga matan nada samari awaje, Ex dina, class mate dina, Classrep dinmu, ko dan office dinta. Cheating a aure yanzu ba yaro ba babba, da sababbin auren da tsofaffin all both mata da mazan nayi. Some mata nada samari awaje while some matan kuma yammata garesu, kunsan mata da yawa na gida are into lesbianism kuwa??? And our Men kusan some of them bada mata suke cheating ba da yan uwansu maza sukeyi??? Like I said, dana tashi yin book dinnan MATAN KO MAZAN I interview ma’aurata da dama, divorcee da Momies wayanda sun haifi kamata, da Aunties, so I decided to pick on the big, big major matsaloli dake kashe aure ayau to write about them in other to Educate yan uwana mata da maza, to show you how to fight that battle and to let you know every problem nada solution, so idan kin dade ko ka dade kana cheating on your partner thinking bazaka iya dainawa ba this book is here to help you overcome this addiction na cheating, I will pieces this Cheating of a thing, the stages and yanda ake dainawa, abinda mutane dayawa basu saniba shine Ma’aurata na cheating ne sabida dalilai da bazasu wuce 1 zuwa uku ba; 1- For revenge, wata feels tunda Mijina is cheating on me I will cheat on him back. 2- Rashin gamsuwa, dayawa maza Dayawan maza cheats because they feel matansu are lacking in a thing or something in za other room, same with mata maybe baya gamsar da ita or he’s too tiny. 3- Addiction, addiction ina nufin wayanda suka saba sleeping around tun kafin suyi aure, so bayan auren bawai suna cheating sabida partner dinsu yarasa wani abu bane ko basa gamsuwa sunayine sabida sun riga sun saba bazasu iya rayuwa da one sexual partner ba, kun gane…. SAIDAI!!! Is not going to be FREE this chapter and I employ each and every one of you to support me, this Chapter two is about to BLOW YOUR MIND💃 Payment is just 1k, pay into 6353995766 M Shakur world Moniepoint saiki turomin evidence of payment ta whatsapp wa.me/+2347012181461 sainai adding naki a PAID GROUP DIN. If you wanna speak to me akan wani abu chat me up a whatsapp 07012181461, ko send a message ta IG @mshakur_world ko tiktok @mshakurr Thank you and I love you remember CHANGE IS NOT EASY just like yanda Hadiza is struggling yanzu ta chanza, baka tashi rana daya ka chanza is process the most important a process din is determination wato JAJIRCEWA!!! 15 Wuraren 2:30 Hadiza tai parking motanta gaban school na su Aman sai kallon gate na school din take she can’t even remember the last time tazo school nan kowani function sukeyi da ake bukatan iyaye saidai Nura yaje ita bata zuwa, Anty Jams dake kallonta tace “sauka kije ciki ki daukosu” ijiyan zuciya tasauke feeling wani iri for the first time all this while taji yes da gaske ne tayi neglecting yaranta sosai, cultural day, parent forum, end of the session party duk wani abu na school dinsu Nura ke zuwa, koda Aman yayi graduation na gama prep Nura yaje hoton Aman yana saniye da graduation gown da babban shi ne kawai a hoton, shiga cikin school din tayi daidai lokacin teachers sun fito da yaran za’a sakasu a school bus bamasu lurada itaba hannunta Hadiza tadaga tana kakalo murmushi tai waving nasu tace “Amali, Aman” dasauri duka yaran suka juyo tareda teacher su dabata lurada Hadiza ba ta taho wajen da sauri tace “ohh sorry Madam ban ganki ba good afternoon Ma” Gyadamata kai Hadiza tayi tana kallon yaranta daketa kallonta da mamaki, Hadiza tamika hannu zata kama Aman yadauke hannunshi da sauri yana turomata baki yana hararanta sai kawai jikin Hadiza yayi sanyi tasa hannu tadauki Amal ajikinta cikeda wayancewa tace “princess İdanun Mommy naciwo saisa sukai ja kinata kallona” teacher tace “no wonder nima I wanted to ask” takalli Aman tace “follow your Momy Aman” cikin dan yake Hadiza na kallon Aman daya dauke kai tace “don’t mind him I don’t know why he’s angry let’s go Aman” tasake miko hannunta wannan karan buge hannun Hadiza Aman yayi saitaji hawaye zai zubomata dasauri cikeda kunya tayi gaba da Amal tace “okay then come on your own tunda bakaso nakamaka” tayi gaba da Amal, ihuu Amal ta kwala tana fizge kanta daga Hadiza tace “leave me I want to go to my brother, Anty Ummi said I should never leave my brother alone koda yaushe muna tare, he’s my best friend leave me Momy” Amal ta tsandala ihu dayasa Hadiza tasaketa da gudu aiko Amal ta fanfalo zuwa wajen Aman dake tsaye akumbure teacher na lallabashi yabi mamanshi, Amal na zuwa ta rungume Aman cikeda yarinta tace “Ya Aman don’t be angry, let’s go, come” Aman dayaki tafiya Amal ta kalla, fashewa yayi da kuka yace “I don’t like her, I don’t want to go with her Princess, she will start shouting very soon” ganin yayanta na kuka sai itama Amal tahau kuka sai abin yafara jawo attention na mutane da sauri gudu gudu Hadiza tajuya tabude mota tashiga takifa kanta kan matukin mota tace “I can’t do this Anty Jams, I can’t, yarinyar nan tariga tayi brainwashing yarana Aman hates me sooo much” dan ijiyan zuciya Anty Jams tasauke batare datace ma Hadiza komiba tabude motan tasauka ta tafi wajen yaran bata wani sha wahalan shawo kansu ba sun santa sosai suna sonta Aman yace “where is Batool?” Murmushi tayi takama hannunshi tace “tana kano, muje gida kunji” binta sukayi bayan tasasu tarife takoma gaba Hadiza tatada motan taja bini bini tana kallon yaran dake wasa abunsu su biyu abaya, gashi kansu ahade they’ve learn to love each other and support each other so well kuma is all thanks to Ummi, parking tayi agaban Burger King tajuyo takallisu cikin kakalo murmushi tace “Amanu zakaci burger and fries muje na siyamaka anan burger king?” Batare daya kalleta ba yace “I hate burger” dasauri Amal cikin zakin murya tace “yes Mommy Ya Amanu doesn’t like burger, Ya Aman likes pizza, chicken pie and hotdogs, nikuma I love shawarma mai 2big sausage irin wanda Anty Ummi kemana ko Ya Aman”? Gyadamata kai yayi yana murmushi yace “muje gida and tell Anty Ummi tamana ko”? Dasauri Amal tace “yesssss Anty Ummi is the bestttttt cook, teacher said if a person can cook is called Chef” atare yaran sukace “Anty Ummi is the best chef” yanda Anty Jams ke kallon yaran haka Hadiza ke kallonsu ganin bazata iya magana ba yasa Anty Jams tace “kaga Amanu Mommy ku zata siyamuku duka favorite dinku tunda pizza kakeso bari aje debonaires ko dodo pizza ko” yana kallon Anty Jams yace “Momy is busy she never take us anywhere” buga Hadiza Anyy Jams tayi aboye hakan yasa Hadiza tanuna kanta tace “Aman I will never be busy for my sweet boy again kome kakeso zan saya maka kaji, pizza da mene da mene kakeso”?Sosai Aman yake kallon Mamanshi kaman yanaso yagane wani abu still dai cikeda rashin sakewa da ita dakuma haushinta yace “pizza and bubble tea na Nutella irin wanda Daddy ke sayomana” gyadamai kai Hadiza tayi feeling a bit better ganin yamata magana yanzu takalli Amal tace “princess ke me kikeso” Shiru Amal tayi tana juya idanu looking super adorable tace “mommy I want a biggggg giant shawarma with ice cream mai cone ba cup ba” murmushi Hadiza tayi feeling kaman ta fashe da kuka tace “okay Baby na Mommy will buy everything dakukeso ko, juyawa tayi dasauri ta tada motan cold stone sukaje dake hade da Dominos pizza nan suka bada order komi suka zauna ana kawo kwalin pizza Hadiza ta karba tana murmushi tajuyo tabama Aman karba yayi yana kallon Hannunta yace “ina na Anty Ummi? Daddy always buy mine and na Anty Ummi” Amal tace “yes me too one ice cream for me one for Anty Ummi, one shawarma for me one for Anty Ummi” duk yanda Hadiza ta daure saiga hawaye dasauri ta share zatai musu magana Anty jams ta girgiza mata kai alamun asayo na Ummi inhar tanason tayi winning yaranta, ahankali tace “Tom bari asayo nata” bada order na Ummi sukayi suka kara jira nan aka gama komi Amal ta karbi na Ummi nan da nan yasaki yana murna itama haka Amal dukansu kowa yadauki nashi da na Anty Ummi suka koma mota Hadiza tashiga motan bayan tasasu abaya sai gida suna kaiwa gida wlh kafin tagama parking da kyau Aman yafice da komi yana shouting sunan Anty Ummi tundaga nan waje Amal biyeda shi. Ummi na zaune adakinta taji yaran na kwalamata kira dasauri ta tashi tafito ko kadan batasan suna tareda Hadiza ba danta dauka Hadiza na wajen aiki bene tayi ta na sauka tana kaiwa last staircase yaran na zuwa wajen da abubuwa a hannunsu cikeda murna suka wani rungumeta. “Oyoyooo Anty Ummi” daidai Hadiza na bude kofan falon tana shigowa suka hada ido da Ummi, faduwa gaban Ummi tayi ahankali tashira cire yaran daga jikinta tace “Aman oya to kuje kucire uniform” daidai lokacin Anty Jams na shigowa Aman da Amal suka bata abubuwan hannunsu “Anty Ummi take ur own pizza” Amali tace “Anty Ummi ni ice cream da shawarma nakawo miki take” daga Hadiza har Anty Jams tsayawa sukayi suna kallonsu cikeda rashin sakewa Ummi ta kakalo murmushi batare data karbaba tace “to kuje ku ijiye a dinning sai aje acire uniform, awanke hannu saikuzo muci tare” Dasauri suka tafi dinning suka ijiye sannan sukazo sukabi gefenta sukai sama da gudu mikewa tsaye Ummi tayi ahankali takalli Anty Jams danta santa ahankali tace “sannu da zuwa Anty, ya hanya yakuma su Batool” danne komi Anty Jams tayi tace “suna nan lpy Ummi” ahankali Ummi tajuya harta fara hawa stairs Hadiza tace “namiki iyaka da yarana baki jiba, kome namiki ke kikaja, kifita daga harkan yarana baki basu” wucewa Ummi tayi sama batare datace komiba Anty Jams ta harari Hadiza tace “ai saiki wuce sama kije ki tayasu chanza kaya, kiyi salla sannan ki sauko ki daura abincin dare tunda girkin ki ne, wuce muje nima bari naje nai salla” duk suka wuce sama. Ummi tanajin yaran na kiranta nabuga kofan dakinta amman takasa amsasu ko fita duksai taji batajin dadin komi dan wlh tanason su Amal bawai pretending ba yaran akwai shiga rai gasu kyawawa sosai. Da taimakon Anty Jams tana kara nunnunama Hadiza wasu abubuwan dan bawai bata iya girki bane tsabagen rashin yi ne yasa ta manta suka dafa lafiyayyen fried rice da peppered chicken suka hada juice yaran sukaci pizza su suna ijiye na Ummi Anty Jams ta tayasu yin homework sai tambayan Ummi suke. Bayan magrib Nura yashigo gidan da sallama dasauri yaran dake tareda Anty Jams suna homework suka taho wajenshi da gudu suka rungumeshi daukansu duka yayi yace “Aman ka kara nauyi wai zaka karya Dady” dariya Aman yayi sosai cikeda son Babanshi yace “Dady ni ban kara nauyiba, Dady where’s Anty Ummi bamu ganta ba” Amal tace “Dady Momy takaimu mun sayi ice cream shawarma and pizza mun sayo mata tace muje mu chanza uniform saimu fito muci tare but munata nemanta we can’t find her” yana kallon yaran nashi with love yace “zan nemota” ihu yaran sukayi suna kara rungume shi yashigo cikin falon cikeda girmamawa ya gaida Anty Jams ta amsa tana murmushi tace “barka da dawowa Nura ya aiki” anatse yace “Alhamdulillah sannu da zuwa, bari naje sama nadan watsa ruwa” tace “to Nura” wucewa yayi sama da yaran manne dashi suna bashi labarin komi daya faru yau, dakin Hadiza yafara bude kofa yashiga tana zaune gaban madubi tana kokarin saka earring tana sanye dawani blue jean da shirt nude mai shegen kyau tayi lafiyayen makes up a fuskanta tana kallonshi ta madubi, yana rikeda yaran yakaraso inda take yana kallonta yace “zaki fitane”?Girgizamai kai tayi tareda juyowa takalleshi asanyaye ahankali kaman ba itaba tace “sannu da zuwa Nuri na” duk yanda Nura yaso boye mamakinshi kasawa yayi yau shine Hadiza ke cema sannu da zuwa sai kawai yasa hannunshi daya yajawota tareda bata side hug yace “kinyi kyau sosai right kids?” Dasauri Amal dake jikinshi tace “right Dady Momy tayi kyau” Aman yaki magana sai kawai Hadiza ta tsugunna gaban Aman tareda shafa kuncinshi tace “bazaka ce Momyn ka tayi kyau ba?” Turo baki Aman yayi yace “kinyi kyau” murmushi sosai Hadiza tayi tace “thank you my first born” kasa boye mamakinshi Nura yayi sai kawai ya ijiye Amal kan gado yace “ku zauna da Mommy ku bari naje nayi wanka nazo” wucewa bayın Hadiza yayi tabishi da kallo cikeda so tana wani kalan jin dadi yanda bai nemi Ummi ba har yanzu Aman wucewa yayi yabar dakin itakuma Amal tacigaba da wasanta ita kadai akan gado wanka Nura yayi yafito ya shirya tsaf cikin jallabiya yanayı yana satan kallon Hadiza dayaga tanama Amal wasa akan gado cikeda mamaki ya feffesa turare sannan yawuce wajen kofa dadan sauri daidai yasa hannu Hadiza tajuyo tace “ina zaka? Abinci is getting cold kai muke jira fa babu wanda yayi dinner” juyowa yayi yasake kallon Hadiza kafin ahankali yace “keda Amal kuje lemme call Ummi sai duk muyi dinner tare” harya bude kofa cikin zafin murya Hadiza tace “Nuri!” Juyowa yayi ya kalleta suka hada ido strictly Hadiza tace “I cooked for you not for her” anatse Nura yace “yau girkin kine Hadiza you cook for the entire house not only me, kuje kasa ganinan” yana maganan bai kara jiran wani magana nataba yawuce Hadiza jitayi kaman ta kama da wuta hannunta da jikinta sun fara rawa na bacin rai knocking Nura yayi gaban kofan Ummi yace “bude kofa Ummi” tashi Ummi tayi ahankali tabude kofa suka hada ido da Nura tayi wanka tasaka wani jan material da aka mata fitted doguwan Riga mai kyau ta daura dan kwalin dan komawa baya tayi yashigo dakin tareda maida kofan yarufe ahankali Ummi tace “barka da dawowa Yallabai, ya yininka ya kasance yau? Dafatan komi yatafi lafiya, ya Hajiya kuma” batare daya bata amsaba yajawota jikinshi warm hug yabata tareda lumshe idanu ahankali yace “komi lafiya lau Babyna, nasan bakiyi dinner ba let’s go” adan tsorace Ummi ta girgizamai kai tace “kaje kuyi idan kun gama zan sauko nayi ni” hade giran sama data kasa Nura yayi yace “kinason nayi fushi dake?” Dasauri ta girgizamai kai anatse yace “da iyalina zan dingacin abinci so wuce mutafi” yayi maganan yana kama hannunta suka fito zare hannunta tayi dasauri daga cikin nashi suka cigaba da tafiya har kasa Hadiza na zaune a dinning hakama Anty Jams da yaran suna ganin Ummi sukai ihuuu suka taso da gudu zuwa wajenta. “Dady a ina kaga Anty Ummi, ina kikaje Anty Ummi” murmushi tamusu tace “muje muci abinci zan fada muku” duk rirrike mata hannu sukayi suka tafi dinning zama Nura yayi Ummi ta zauna kan kujeran dake kusadana Amal Hadiza kaman kartai serving abincin but bataso tabatama Anty Jams rai hakan yasa tashiga zuxzuba abincin, Nura tafara zubamawa tazubama Anty Jams ta zubama Aman da Amal sannan tazubama kanta ta maida kulan tarufe Anty Jams tama Hadiza wani kallo da idanu ta dauke kai kaman bata ganta ba nura baice mata komiba daga plate nashi yayi yamikama Ummi yace “ci abinci” saishi yatashi yadauki plate yashiga zuba wani Hadiza namai wani kallo zuciyanta na tafarfasa tass Nura yagama diban iya abincin da zaici ya zauna saikuma yakalli Ummi dayaga takasa taba abincin babu wasa kan fuskanshi yace “nace kici” gyadamai kai tayi ahankali tadauki spoon ahankali Aman yace “Anty Ummi eat dady food have plenty chicken” debo abincin Ummi tayi ahankali zatakai baki Hadiza ta mike batai wata wata ba ta kabar da spoon din cikin tafarfasan zuciya tana huci tace “ke har kin isa sabida you are shameless nama mijina girki kice zakici wulakantacciyan yar aiki irinki eh, nazauna akan dinning da ni da family dina kema kizo ki zauna zakici abinci tareda mu bar wajen nan!” Hadiza tai ihu dayasa Ummi ta yunkura zata tashi chak Nura yakama hannunta yace “sit down and eat nace” yasake daukan spoon nashi yasa a abincin yace “zauna” zama Ummi tayi ahankali, azuciye wannan karan Hadiza tasa hannunta tadaga plate na abincin Ummi ta kabar akasa tace “dakici abincin nan Ummi gwara yayi asara” cikin fushi Nura yace “Hadiza!” Itama cikin fushi Hadiza takama waist dinta tace “Nura! Miye?! Wat!” Cikin tsananin fushi yace “this is the second time kike wulakanta abinci agidan nan kinsan mutane dubu nawa ne yanzu aduniyan nan da basu sami kalan abincin nan sunci ba? Kinsan hukuncin maiyin annubazaranci da abinci kuwa?” Cikin tsantsan tsananin fushi tace “I don’t care Nura all I know is yarinyar nan bazataci abincin dana tashi nashiga kitchen na dafawa mijina ba wlh” ahankali Nura yace “okay ni kika dafamawa ko nima bazanci ba ki tattara komi kici” yayi maganan yanajan hannun Ummi zai wuce Hadiza tasha gabanshi tace “Nura for how long ban maka girki ba? Kullum korafinka is ban maka girki ba, yau nashiga kitchen dakaina na ijiye komi and cook lafiyayyen abinci for you amman kana barin abincin sabida this stupid girl? Nura kai har ka isa namaka girki kafasaci sabida wata banza? Wai waye kai kakejin wannan isa isan da takama takaman how dare you Nura Hadiza ta shiga kitchen tamaka girki and leave the food for her”? Cikin fushi Anty Jams ganin Hadiza harta manta da duka fadan da tamata dazu tace “Hadiza!” Cikin fushi Hadiza tace “Anty Jams don’t call me please don aganın gaban idanunki shiya fara, shine neman fadana, namaka girki sabida kai bakın makiri ne, munafuki, annamimi saikabar abincin matarka sabida yar aikinta wani kalan bakın dan iskan mugu ne kai Nur……..” jikake tasss! Anty Jams ta zubama Hadiza mahaukacin mari da saida Hadiza taga stars dasauri Hadiza ta dafe kuncinta tana kallon Anty Jamila cikeda mamaki dake huci tace “Anty Jams” cikin tsananin fushi Anty Jams tace “what kind of a woman are you Hadiza kina zubawa mijinki zagi haka? Kinsan hukuncin mata mai zagin mijinta kuwa??? Duk matan dake zagin mijinta wutan lazza ake sata ranan gobe kiyama, what’s all this childish behavior? Ke wace kalan fitinanniyan, masifaffiyan mata ce Hadiza yar bala’i are you from ghetto? Must everything be handle with violence awurinki? Kina tunanin ihu da zagi da haukan nan dakikeyi will solve anything for you?” Cikin serious fushi Anty Jams takalli Nura tace “And you what is wrong with you Nura are you even a man? Akan mene zaka dinga taking this nonsense from this girl bazaka mata shegen duka ba ka farfasa mata baki? Waye Hadiza duka dukanta guda nawa take? Nura wannan ba shiru shiru bane sannan ba hakuri bane this is a disease ke damunka, bazan maka karya ba kaika bata Hadiza to this extend datakeyin yanda taga dama cus tasan bazaka mata komiba? Kana ganin soyayya kake mata haka tana irin haukan nan kamata shiru and let her go free? Nura are you a child da matanka zata dinga zaginka haka?? No Nura ko kanina na jini bazan yarda matansa na zaginshi hakaba wlh Nura, bazakai punishing Hadiza ba if she’s not ready tayi zaman aure dakai ka saketa and chase her out taje and experience life maybe tayi learning lesson nata, Nura I seriously hate the way settings na gidanka is going, enough please you need to wake up for once kayı acting like a man kaci uban marakuyan yarinyar nan, common Aman da Amal kuzo muje mu kwanta wlh gwara na kwana da yunwa danaci abincin chan Thank God akwai pizza and shawarma asama” tawuce sama fuuuu su Aman duk suka bita itama Ummi wucewa sama, Nura yadade yana kallon Hadizan dahar lokacin take rikeda kuncinta kafin yawuce sama shima fuuuu, wasu hawaye masu zafi ne suka fito daga idanun Hadiza tajuya takalli dinning din abincin kowa na wajen sai kawai ta zauna akasa wajen tafashe da kuka sosai tace “shikenan babu mai sona aduniyan nan, ba yarana ba, ba mijina ba ba yayata ba wacce mukafito ciki daya, why is it that nobody is willing to understand what am going through anan? Mijina yaci amanata yaci amanata, ya auromin yar aikina batare da saninaba, ance kaza kaza yasa yamin kishiya sabida bana this and that which na yarda, I tried my best to change Allah yaga zuciyana I cooked this food with so much love for Nuri, I cooked it with love for my husband to please him and to show him I’ve changed but yakama yazomini da wata, what is wrong because na nuna ba ita nama girki ba? Karya nayi? Ita nama girkin? Akanme zanyi pretending nabawa wacce na tsana abinci? Why am I not allowed to express myself, to express my feelings, to express my anger, anmin laifi an dakeni yanzu kuma ance ban isa nayi kuka ba, ba’a ganin laifin yar iskan shameless yarinyar dahar tanada guts ta sauko tafito tazo tazauna a dinning tace zataci abincin mijina, nayi serving mijina abinci yadauka yabata sabida tantiriyan mara kunya ce tadauka zataci akanme zan barta? Godddddd Ya Allah! Maisa nobody is looking at things daga my own perspective? I love Nuri with everything I got and I hate wata atare dashi banda ni, God oooo why are you tasting me this way?? Maisa ban mutu gabaki dayaba na huta cus at this point banjin I can continue living in this agony and sorrows ba gwara na mutu, no one is supporting me wayyooo Allah zuciyana” tai maganan tana wani irin kuka mai sosa rai tana buga kanta abango Nura da all this while yana staircase tsaye yana jinta jikinshi yayi sanyi wani kalan tausayin Hadiza yake bana wasaba he will say this again and again baitaba sanin wannan reaction din zaiyi getting from her dayay auren nan ba, yadauka still halin ko oho, I don’t care dinta zata cigaba dayi cus yasan baya gaban Hadiza at all, she no just send him ne at all but all he’s getting is total opposite of abinda yayi expecting from her is as if auren nan daya kara awoken feelings dinshi in her heart banda haka yakara mata wani strong love nashi azuviyanta yanaga sisters to be honest he hates seeing any mace in pain balle kuma Hadizan shi. Yadade awajen sannan yashiga saukowa kasa Hadiza na kuka sosai bin stairscase din tayida kallo ganin Nura ne ke saukowa saita kara kara karfin kukanta ko kallonta baiyiba jitayi kaman ta mutu dinning ya wuce hannu yasa yadauki plate na abincin yadawo ga mamakin Hadiza zama yayi anan kasa agabanta ya ijiye abincin da bottle water ahankali ya debo rice din yakai bakinshi tareda lumshe idanu yace “uhmmm delicious” wani irin tsumewa da kuka Hadiza tayi mai kashe zuciya tana kallonshi tanajin wani irin so dabata taba sani tanama Nuri ba, kusan 5spoon yayi sannan yadebo yakai bakinta yace “eat is very sweet” hawaye na zuba daga idanunta tabude bakinta ahankali yasa mata taunawa tashigayi ahaka tana kuka sosai yake feeding nata har saida shi da ita suka cinye abincin tass yasha ruwa yabata ragowan tasha still hawaye sun kasa daina zuba daga idanunta tashi yayi yakai plate din kitchen ya man maida sauran abincin flask yadauki broom ya share shinkafan kasa tass ya kashe wutan falo yazo ahankali yadagata wlh bamata da karfi ahankali yadauketa chak a jikinshi Hadiza takasa daina kuka son Nura datakeji kaman zai hallakata haka takeji dakinta yabude yashiga da ita tareda maida kofan yarufe ya kashe wuta yayi gado da ita ahankali ya kwantar da iya yana kallon fuskanta da side lamp dake wajen kaman yanda take kallonshi yunkurawa yayi yatashi zai wuce tarike hannunshi karaf hakan yasa yajuyo yakalleta tana kuka in a very very vulnerable state cikin tsantsan so da narkewan zuciya tace “Nuri I’m sorry! Nuri I’m so soo sorry! Nuri kayafemin kaji” kusan mutuwan tsaye Nura yayi Hadiza fa is unapologetic so is he dreaming datake cemai ya yakuri, cikin kuka tace “Nuri bazan iya rayuwa without you ba cus u are my entire life, you gave me happiness, peace and freedom, Nuri u are the best man aduniyan nan and I love you with every every thing in me, Nura I love you a whole lot” yana kallonta still har lokacin cikin kuka tace “I know I’ve been a pain in your ass, I’ve been nothing but trouble, Nura I know am very stubborn but stubbornness dina baya nufin ban sonka wlh ina sonka kishi ne ke dawainiya dani nakasa coming to terms with yarinyar chan matankace my heart is heavy Nura help me I don’t think I can do this alone” gently Nura ya kwanto kan jikinta tareda daura fuskanshi kan nata ahankali cikeda so yace “Hadiza!”Cikin sheshekan kuka murya chan kasa tace “Nuri na! Dan darajan Allah kasaki yarinyar nan banson na haukace gabaki daya, wallahi wallahi zan chanza bakaga yau dakaina naje na dauko yaran nan ba, I took care of them na saya musu pizza I did everything sannan nayi girki, wallahi Nuri I will change and become a good wife, I will give you all my love, na kula da kai and give you the best of the best cus kaine sanyin idaniyata, please Nuri promise me zaka saketa” girgizama mata kai yayi murya chan kasa yace “I can’t Hadiza! I can’t” yanda take kuka dazakaji saika mata kuka murya Chan kasa Nura yace “son da nake miki babu abinda yaragu koya sauka, bazata taba iya sa narage sonki ba, har yanzu Nura is very much your own, just take care of me, give me all your love, pamper me nobody can come between us I promise you this, I am yours, yours only Hadiza, Nura naki ne sai yanda kikai dani circle dina dake mubiyu ne kadai ciki ki kuladani batare dakin kawo kowaba I want you to be blind akaina ki manta inada wata matan, uhm babyna” yay maganan yana manna mata kiss kissing juna sukahau yi yana bude wandonta yadago tareda ja kasa ya yar yacire jallabiyanshi ya yar da boxer yadagota itama yana ciremata riga grabbing her boobs yayi squeezing da kyau kwantar da ita yayi yahau kanta yakai joystick nashi bakinta zai saka ciki yace “s*ck me” juyarda kanta tayi dasauri cikin raunanniyan muryanta tace “Nuri kasan banson inashan gaba fa is somehow abakina, yana sani inji kaman am about to puke” bai damuba yakoma baya yadaga kafafunta yakai kanshi zaisha mata down there da sauri ta fizge kafafunta tace “wannan wani irin barbaric fettish ne haka Nuri? You see abinda nake fadi ko kaga abubuwan da karuwan yarinyar nan takoya maka ko” dagowa yayi strictly yace “stop calling her with that name” zata kara magana yahada bakinshi da nata kawai ya danna mata shi ciki, forget Nuri nada dan shekaru but he’s still good in bed, he f*cked Hadiza so good tafara neman kwace kanta dan to be honest Hadiza ba sex freak bace, batawani damu da sex ba ita ganin sex take as damuwa, tun tana daurewa Nuri na different styles da ita tanajin dadi har abun ya gimsheta zaiyi wheelbarrow da ita ta fizge kafafunta cikeda korafi tace “wai Nuri yaushe kadawo jarababbe ne haka? Are you a monster mehaka kawani babbaremini kafafu, kadage kana abu daya saikace aljanna ake rabawa awajen, please kabarni haka nai bacci is almost 2AM nadare haba kafayi first round” hannunta tasa ta tureshi tareda fizge kafafunta tajuyamai baya kawai yayi shiruuuu yana kallonta rikeda boner dinshi a hannu tana nishi, maganganun Anty Jams ne suka dawomai fill arai he needs to show her he’s d man, hannu kawai yasa ya fizgota a zuciye yana kama kafafunta dasauri Hadiza tace “mehaka Nuri”? Da karfi ya shigeta yafara riding nata crazily tana kokawa dashi almost 15min yayi yasamu yayi exploding yasaketa tareda kwanciya gefe yana maida ijiyan zuciya Hadiza sai tsoki take ta tashi tawuce bayi tayi tsarki tadan gyara kanta, wato haka yakeyi da yarinyar chan Nuri da baida jaraba sai suyi wata babu abinda yashiga tsakanin su, idanma zasuyi one round shikenan but jibi Nuri yau kaman maye, fitowa tayi tazo ta kwanta gefenshi taja bargo sai bacci. Kun tuna albishir din danace zan muku yau???🥰 Here we go, MATAN KO MAZAN chapter 1 is coming to an end just few more episodes to go which nakega zan gama mukushi within this week now here comes the EXOTIC NEWS konace the most EXCITING PART of the news shine Chapter II namu wanda is about CHEATING!!!! Did you know acikin kaso dari na ma’aurata 90% na cheating?? Ko kiga mijin yanada babes awaje ko kiga matan nada samari awaje, Ex dina, class mate dina, Classrep dinmu, ko dan office dinta. Cheating a aure yanzu ba yaro ba babba, da sababbin auren da tsofaffin all both mata da mazan nayi. Some mata nada samari awaje while some matan kuma yammata garesu, kunsan mata da yawa na gida are into lesbianism kuwa??? And our Men kusan some of them bada mata suke cheating ba da yan uwansu maza sukeyi??? Like I said, dana tashi yin book dinnan MATAN KO MAZAN I interview ma’aurata da dama, divorcee da Momies wayanda sun haifi kamata, da Aunties, so I decided to pick on the big, big major matsaloli dake kashe aure ayau to write about them in other to Educate yan uwana mata da maza, to show you how to fight that battle and to let you know every problem nada solution, so idan kin dade ko ka dade kana cheating on your partner thinking bazaka iya dainawa ba this book is here to help you overcome this addiction na cheating, I will pieces this Cheating of a thing, the stages and yanda ake dainawa, abinda mutane dayawa basu saniba shine Ma’aurata na cheating ne sabida dalilai da bazasu wuce 1 zuwa uku ba; 1- For revenge, wata feels tunda Mijina is cheating on me I will cheat on him back. 2- Rashin gamsuwa, dayawa maza Dayawan maza cheats because they feel matansu are lacking in a thing or something in za other room, same with mata maybe baya gamsar da ita or he’s too tiny. 3- Addiction, addiction ina nufin wayanda suka saba sleeping around tun kafin suyi aure, so bayan auren bawai suna cheating sabida partner dinsu yarasa wani abu bane ko basa gamsuwa sunayine sabida sun riga sun saba bazasu iya rayuwa da one sexual partner ba, kun gane…. SAIDAI!!! Is not going to be FREE this chapter and I employ each and every one of you to support me, this Chapter two is about to BLOW YOUR MIND💃 Payment is just 1k, pay into 6353995766 M Shakur world Moniepoint saiki turomin evidence of payment ta whatsapp wa.me/+2347012181461 sainai adding naki a PAID GROUP DIN. If you wanna speak to me akan wani abu chat me up a whatsapp 07012181461, ko send a message ta IG @mshakur_world ko tiktok @mshakurr Thank you and I love you remember CHANGE IS NOT EASY just like yanda Hadiza is struggling yanzu ta chanza, baka tashi rana daya ka chanza is process the most important a process din is determination wato JAJIRCEWA!!! 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣6️⃣ As usual da asuba yatashi yawuce bayi wanka yayi yafito ya shirya tsaf cikin jallabiya sannan yazo bakın gadon yatadata ta hanyar dagota yana kallon her sleepy face yace “Hadiza” bude idanunta tayi takalleshi ahankali, softly yace “tashi kije kiyi wanka kiyi salla, fix something for breakfast and get the kids ready for school” dudda baccin dake idanunta but jin ayyukan daya lissafo mata saida tabude baki zatai magana saikuma tai shiru tunawa da fadan Anty Jams, ga mamakin Nura dan he was expecting her to nag sai yaga ta gyadamai kai tace “to” wani irin sweet smile yasaki baisan lokacin daya sumbaci goshinta ba yamike yawuce yafita daga dakin Hadiza tabishi da kallo wani wutan sonshi na ruruwa aranta, tana zaune awajen taji yabude kofan dakin Ummi wani irin bakın ciki taji yataso mata batasan sanda ta runtse idanunta gam gam ba, kasa motsi tayi awajen chan saitaji yabude kofan yafita ahankali ta tashi tawuce bayi tayi duk abinda zatayi tafito ta shirya cikin wani jean da riga mai kyau tasa dankunne tai salla tafito tana zuba kamshi tayi dakin yaranta Anty Jams tagani tana shafama Aman datama wanka mai, kallo daya tamata tadauke kai maida kofan Hadiza tayi tarufe tazo wajen ahankali tace “ina kwana Anty Jams” sabida Aman Anty Jams tace “fine” takalli Aman tace “greet Momy ka” batare daya kalli Maman ba yace “good morning Momy” shafa fuskanshi Hadiza tayi tace “morning Son” karasa sakamai kaya Anty Jams tayi tace “jeka wajen Amali” wucewa yaron yayi yafita daga dakin Anty Jams tamike zata fita dasauri Hadiza takama hannunta tace “Anty Jams idan kikai fushi dani rayuwan zata kara zama baki kırın agreni, the husband i have dazan iya magana dashi shine yasani in this situation, I can’t tell my friends abinda yasameni they will just laugh suce banida any influence agidana, kene komi nawa Anty Jams dan Allah kiyakuri, Anty Jams wlh, wlh naji maganan ki, I tried so hard jiyan nan na danne nakasa, look at it fa nashiga kitchen nama mutumin nan abincin dayay shekaru yana complain banamai, saiya dauka yabama wata is it fair? Nura namin mugunta da baki gani sabida anganshi shiru shiru? Anty Jams I can’t pretend to even save my own life maisa kikeso nayi pretending kaman everything is cool? Why do you want me to pretend as if is okay yadauki abincin dana dafamai, na zubamai yabama shegiyan butulun yarinyar chan eh? Why do you want me to pretend??” Juyowa Anty Jams tayi dasauri takalleta ta hanyar rage murya yanda babu wanda zai jiyosu tace “sabida as a woman dole ki koyi pretending, faking it da sauran su you have to learn ai shine kissa da kissisina, yanzu take a look at this girl ba lallai bane tanason yaranki tsakani ga Allah ba but yanzu idan zaki shekara kina gayama Nura Ummi batason yaranshi bazai taba yardaba why? Because dudda tana yar kauye ta iya wasan? Agaban babbansu zata iya nuna tafison yaran nan sama da rayuwanta, Hadiza u are educated but u lack wisdom, bakida hikima ko kadan, bakida dabara bakida wayau, waya gayamiki being real pays a zamanin nan da ake? Kowa is faking it pretending to be who he’s not, Allah kadai yasan waye mu sabida shine kadai yake duba zuwaga zukatanmu, you always allow your heart to control you baki using kanki, head is a monster while the heart is a toy very fragile, wani zubin is good to use head, idan u wanna catch Nura a palm na hannunki you need to stop showing him kin tsani yarinyar nan, and you have to stop being razz, loud and mahaukaciya like attitude nakin nan, yanzu yanda kike so hyper nan yarinyar nan bazata taba fito da true colors nata ba sabida Nura yaganta for who she is, amman idan kinaso to expose her inner aim you need to calm down make peace da kowa the ball is in your court har yanzu, wlh Nura na sonki Hadiza, I keep saying it kada ki bari soyayyan nan ya gushe, control anger naki, learn to swallow pride da kishinki sometimes not everything must be said, ki iya kissa da kisisina ki iya buga siyasa, idan kika kara all this attribute akan knowledge dinki wannan yarinyar saidai tazama yar kallo agidan nan wlh kinajina”? Ahankali Hadiza ta gyadamata kai, saikuma ahankali tace “Anty Jams yanzu yau saina bata breakfast na safe”? Gyadamata kai Jams tayi tace “da nine kema dakaina zanje nakirata bazan bar Nura yakirata ba, Hadiza show this girl she can’t play with you, Kece the real mastermind na game din nan, you set the rule, Nura is yours kinaji, ki nunama Nura love agabanta itama ta shaka, nasan hala tanachan maybe tanajin dadin kunyi fada yau Show her keda Nuri baku iya fushi da juna kinji” Dan murmushi Hadiza tayi abun na shiganta tace “to, yanzu mezan dafa for breakfast”? Anty Jams na mata wani kallo tace “Hadiza ohh Allah, da gaske kin dawo tantiriyan yar iskan yarinyar kin manta girke girken abincin safiya dakikeyi agidan ubanki ko to jeki tambaya YouTube, shegiya rubabbiyan fandararriyan yarinya” dariya Hadiza tayi tawuce tafita daga dakin tana hararan kofan dakin Ummi tadauka kasa. Kitchen tashiga tafara aiki, bawai wasaba jitake kaman ta kurma ihu kaman zata zare haka takeji, dudda tanada kitchen tools that made cooking so easy but nahhh! She hate this cooking thing, tana cikin kwashe chips daga air fryer akai hugging nata tabaya dasauri ta juyo hada idanu sukayi da Nura da sauri ta turomai baki kaman yar yarinya tace “good morning” wani irin murmushi yamata dake kashema Hadiza zuciya yace “sannu da aiki Madam Boss Lady, Hajiya Hadiza damusan gida” murmushi tamai saikuma tace “bahaka kakeso na shiga kitchen naita wahala ba look at the way naketa zufa? Nuri why all this stress bayan Allah ya horemana baka ganin yanda business partners naka a living agidansu, why at my age and stage of life zan dinga shiga kitchen when I can hire the Guinness world record breaker Hilda tazama cook dina agidan nan ko wata or wani famous Chef, when the money is not an issue why stressing me Nuri?? Look at yanda nake zufa is it fair?” dasauri Nura yasaketa yana wani kallonta from head to toe saikuma yarike baki yace “dole nasaka miki AC guda uku a sabon kitchen dinki na sabon gida come here my lioness” sai kawai yajawota jikinshi taredakai hannunshi yana sharemata dan zufan daya keto mata daga goshi yace “bari me kikeso natayaki yi?” Bata tabajin dadin tambayanshi kaman na yau ba dudda tasan he’s just trying to block maganganunta ne yasa dasauri ta rungumeshi kaman zata shige jikinshi tace “just kaimin flask dinnan dinning kazo kaji” sakinta yayi yace “to Madam” daukan flask din yayi like a gentleman yawuce yafita dashi yakai dinning ya ijiye ya tsaya daganan yana kallon yanda take aiki a kitchen tana yatsine fuska yana fada da every tool dazata dauka he just wish Allah sa tadaure ahaka and he feels like appreciating and encouraging her, dan jim yayi saikuma ya ciro wayanshi daga Aliiyu ya shiga danne danne Hadiza na cikin aiki a kitchen taji wayanta yayi kara dasauri ta ijiye abinda tarike tazo kan island tadauki wayan kawai taga alert of 5M from Nura ansa narration as gift, dasauri tajuyo da kanta hada idanu sukayi yadan dagamata gira dawani irin sauri tazo kawai ta rungumeshi tace “Thank You Nuri na, you are just the best husband” murmushi yamata yace “and you are the best stubborn wife” dariya tayi kaman ba itaba taja hannunshi tace “kasan menene Nuri inaso nayi running sales na duka items dake shagona 30% off, nasan customers dina will rush everything zasu saye tass inaso nakawo new designs na kaya da turaruka harda kudin nan daka bani zan kara in kawo new abubuwa da yawan gaske nadan kara furnishing shagon, sales din saiya zama strictly online sales no walk in sabida muyi gyare gyaran da fentin da kyau” Gyadamata Kai yayi yace “okay Allah bada sa’a, if you need more fund along the line just let me know” murmushi tayi tare suka karasa aikin suka fito da komi yaran da Anty Jams suka sauko adan kunyace Nura ya gaidata zai wuce sama Hadiza takama hannunshi ahankali tace “Ina zaka?” Yana kallon kwayan idanunta yace “zan kira Ummi muyi breakfast” wani kalan daci taji aranta amman saita daure tajawoshi tazaunar dashi tace “don’t worry I will call her ai komi yawuce, nariga namaka alkawari dakai da Anty Jams I will never cause trouble again” Sosai Nura ke kallonta, murmushi Hadiza tamai tashafa kirjinta tace “trust me” tamike tawuce staircase Nura yabita da kallo tundaga kan staircase tafara kwalama Ummi kira, “Ummi, Ummi baki tashi bane breakfast is ready” sakın baki Nura yayi hakan yasa Anty Jams tace “Hadiza is a good person Nura kawai tana sonka ne over, and is not easy coping with kishiya but zaka gani eventually komi zai daidaita just try and be just, sannan caution duk wacce zatai misbehaving” gyadama Anty Jams kai yayi. Hadiza tana kaiwa gaban kofan ta tsaya tai jim saikuma takai hannu ahankali zata bude kofan Ummi tarigata budewa hada ido sukayi da sauri Ummi tasauke kanta kasa ahankali tace “Anty yakuri ina cikin bayine dakike kirana ina kwana, gani” Hadiza dake kallonta daga sama zuwa kasa hijabine ajikinta jitayi kaman ta shaketa tadai daure iya daurewa tace “bismillah zomuje muyi break” dadan sauri Ummi tadaga kanta takalli Hadiza, Hadiza tace “muje mana, kosaina kama miki hannu”? Dasauri Ummi ta girgizamata kai Hadiza tajuya zata wuce dan she can’t stand looking at the girl dasauri Ummi takama hannunta ahankali tace “Anty” tsayawa chak Hadiza tayi batare data juyoba, fitowa Ummi tayi daga dakin gabaki daya tareda jawo kofanta tarufe ahankali Ummi tace “Anty dan Allah kiyakuri kome namiki ki daina fushi dani, gidan nan gabaki daya ba dadi idan ranki yana abace, wlh niba muguwa bace ko butulu bazan taba cutardake ba, bansan dawo da magana baya amman ban auri Babban su Amal dan cin amana ba na au…….” Dasauri Hadiza tace “kin aureshi dan kina sonshi ne ko?” Tajuyo tazubama Ummi idanunta dahar sun kada sunyi ja hakan yasa Ummi tayi shiru, murmushi Hadiza tasake kakalowa tace “ai kin sanar dani ranan nan wuce muje muyi breakfast” Hadiza ta fizge hannunta tayi gaba da sauri cus idan takara 2secs zata iya hallaka Ummi halan, ba karfi a guiwan Ummi tashiga saukowa har kasan Nura yabisu da kallo yanajin wani kwanciyan hankali zuwa Hadiza tayi tazauna kusada shi Ummi tazo taxauna kusada Aman bayan ta gaida Nura da Anty Jams Nura sai kallonta yake yana murmushi Hadiza na lura dashi, zubama kowa abinci tayi ta zubama Ummi ma, Nura sai mamaki yake aka shiga cin abinci, da gangan Hadiza tawani kwanto jikin Nura tana nunamai ketchup dake gefen lips nata tace “Nuri ohh noo sharemin ketchup a saman bakina” batare daya kawo komiba ya yagi tissue yakama kanta yashare mata yace “har yanzu baki daina shan ketchup ba saikace wata yar Karaman yarinya” cikeda son gumama Ummi Hadiza tace “ni ai babyn kane har yanzu right” adan kunyace Anty Jams tace “Ana kirana awaya nidai bari naje sama nasan su Batool ne” dariya Hadiza tayi tasa chips abakinta tawani yi grabbing face na Nura unexpectedly tace “haaaaam bude bakinka kaci” dan kallon yaranshi Nura yayi dake magana da Ummi datayı kaman bataga komiba tana dan hira dasu tana basu chips nasu abaki, cikin whispering cikeda kunya Nura yace “wat is this Hadiza? Children are he……” kafin yakarasa maganan tawani manna bakinta kan na Nura ta turamai Irish din ciki cikeda iskanci, wani kalan wawan kwarewa Ummi tayi dasauri Nura ya juyo yakalleta yana hadiye chips din da Hadiza ta zubamai abaki dayawa bakinshi yacika tam yace “ummm sorry Ummi” maganan shi ma baya fita da kyau, zai bata ruwa Hadiza tarigashi tace “ga ruwa Ummi sannu halan su Aman sukasa kika kware” karba Ummi tayi daidai lokacin schoolbus na zuwa kwasan yaran yazo duk suka mike from dinning kowa najan lunchbag nashi, Nura yatashi yakaisu waje suka fita Hadiza ma ta tashi daga dinning din tayi wajen kofa akabar Ummi kadai awajen atare suka shigo falo suna shigowa kaman ba Hadiza ba tawani tsalle tahau bayan Nura tana ihu kaman yar karaman yarinya tace “kaini dakina Nuri muje muyi wanka kaine zaka saukeni a shago yau I don’t feel like driving” dan satan kallon Ummi Nura yayi kanta akasa ga Irish agabanta daba wani ci takeba ba yanda ya iya yace “muje” dan baiso yace tasauko yabata kunya ga Ummi awajen suka wuce sama Hadiza na counting step, “bene one, bene two, bene threee…waiii Nuri shillani zan fadi…….” wani hawaye masu dumi Ummi taji sun zubomata daga idanu, kawai saitaji yau kaman ita bakomi bane awurin Nura ba, sai taji wani tsoro, shakku da fargaba sun dirku aranta na kada yazo yasaketa fa dama Hadiza tabata 2weeks gashinan sun shirya yasoma mantawa da ita sai wasan soyayya suke agabanta itada bata taba ganin ya goya Hadiza ba tunda take gidan nan, share fuskanta tayi da bayan hannu dasauri, tama kanta alkawari koma menene tashigo gidan nan kenan Billahillazi La’ilahaillahuwa, zatai kome zatayi Nura itama yasota sama da yanda yake jinta aranshi yanzu, duk yanda taso kada tayi kuka kasawa tayi dan wani daci daci takeji tundaga bakinta har duka jikinta kaman taci shuwaka ganin yanda Nura no even send her today soyayya da wasa sukeyi agabanta, haka ta dinga taba abincin tama kasaci sai kawai ta tashi tayi clearing table din takai komi kitchen tashiga gyara kitchen din just to forget dacin datakeji. Har daki Nura yawuce da Hadiza tana bayanshi sai dadi takeji kaman an mata busharan Aljannatul Firdaus, ga mamakinta bayi yayi da ita daidai zai bude kofa tace “ai nayi wanka sauke ni anan Nuri” batare daya sauketa ba ya bude bayın yashiga yace “nima ai nayi wankan but ba cewa kikayi muje sama muyi wanka tare ba” yayi maganan yana shiga ciki da ita dasauri ta diro daga bayanshi zata wuce tafita ya fizgota tareda mannata abango yace “dawo nan” dasauri takalleshi zatai magana yakai yatsanshi kan lips nata hakan yasa tayi shiru kafin gently yakai hannunshi yashiga cire boturan riganta dasauri takama hannunshi tace “Nuri wai mezakamin? Wlh nagaji Nuri you know very well ni ban wani cikason takura ba tun farkon aurenmu why all of a sudden kadawo this type? Kayi shekaran jiya, kaji jiya yanzun kuma again haba Nuri”? Yana kallonta yace “mesa bakiso? Bani miki dadi ne”? Wani takadirin kallo tamai saikuma ta turo baki tace “ni har yawa dadinka yakemin, kawai Nuri na tsani nayita jika gashina ne every now and then kasan I can’t blow dry gashina dakaina ni kenan kullum naita zuwa saloon sabida kar gashina yayi tsami har yanzu gashina da danshin ruwa fa na dazu” bakinshi yakai saitin nata murya chan kasa yace “koma mezakice kice u can’t escape, I must f*ck you abayin nan aike kika kunnani” Hadiza naughty dariya tayi tace “sannu fire, you such a bad ass man Nuri wlh ka lalace, you’ve rotten” wani fizgota yayi jikinshi yana jan jeans nata kasa saikuma ya mannata abangon yana daga hannunta sama ya danne a tiles kawai yasakin musu shower na ruwan sanyi, ihu Hadiza ta tsandara Nura ya kyalkyace da dariya yana sliding in, Hadiza tace “you so wicked Nuri, ga cold water gaka kuma habb…….” Kasa magana tayi sabida wani twist and turn da Nura yamata aciki sai kawai ta kankameshi, almost 30min suka bata abayin sannan sukayo wanka suka fito zama yayi bakın gado kusada ita yana kallonta tana shiryawa yace “zanje na dauko Hajiya nadawo da ita nan gidan kaman daga sama Hadiza taji maganan wlh saida gabanta yafadi dasauri takalleshi, yana kallonta yace “please don’t give me any more trouble kinji Hadiza? Hajiya bata da matsala, idan tazo just apologize to her and komi yawuce okay” gyadamai kai tayi ahankali tace “tom” murmushi yayi daidai yagama sa kaya yamike yace “yi maza ki karasa shiryawa ki sameni awaje bari nama Anty Jamila sallama” gyadamai kai tayi yana fitowa dakin Ummi yabude yashiga but bata ciki saukowa yayi dasauri jin motsi a kitchen yasa yayi kitchen dasauri adaidai kofa ya tsaya juyowa Ummi tayi takalleshi suka hada idanu ahankali tace “barka da fitowa” saikuma ta daukekai tacigaba da goge gogen datake, jin yayi shiru yasa batare data kalleshi ba tace “me kakeso nadafa maka yau”? Sosai Nura ke kallonta she looks so cold yau, shiga kitchen din yayi yakarasa inda take ya tsaya dab da ita normally yazo close to her like this tana daina aikin datake amman wannan karam saita cigaba da sauri sauri ma, ahankali yace “Hajiya Ummi” batare data daina abinda takeyi kota kalleshi ba tace “uhm na’am, nace mezan dafamaka y…..” hannunta daya kama yarike yasa takasa karasa maganan ta tsaya chak batare data juyoba, murya Chan kasa dake kashe zuciyan mace yace “meya faru baby na? Fushi kike da mijinki eh Ummi na? Akalleni mana” ga mamakinshi fizge hannunta tayi da gudu tawuce kofan kitchen tabude tafita backyard taje wajen bango kawai ta kifa kanta abango tana kuka kaman yar yarinya yana jiyota daganan kitchen, ijiyan zuciya Nura yasauke aranshi yace “ijiye mata biyu ashe is this energy draining, double responsibility, double valaba” wucewa yayi ahankali yabita yaje inda take tana kukan ahankali yadagota yace “waya tabamin ke menene menayi ma gimbiyar matan duk duniya?” Cikin kuka Ummi tace “bakamin komiba ni kawai kewanka nakeyi” saura kadan Nura ya kwashe da dariya yadai daure yayı shiru dan yasan kishin yanda ya goya Hadiza agabanta suka barta dinning ita kadai kesata kuka, cikeda dabara kaman dan yaro age dinta yace “to ai ganinan yau ni nakine ke kadai, haba Babyn Nura, Hajiya Ummi ikon Allah, eh ya isa daina asaran hawayen nan please” yayi maganan yana goge mata fuska wani kalan narkewa tayi ashagwabe tana kallonshi tace “kana sona Dadyn Amal”? Dasauri yace “mesa kika tambaya wannan tambayan”? Kaman zata fashe da kuka tace “ni kabanı amsa” murmushi yamata yayi cupping face nata yace “ina sonki sosai Ummimy, Ummuke Matar Nura” murmushi tamai tace “to shikenan” hugging nata yayi gently to his chest yana patting bayanta yace “kada ki kara tunanin bana sonki kinji shaidan ne now stop crying kimin girki mai dadi yanzu zanje na dauko Hajiya, kada ki kara tunanin bana sonki” gyadamai kai tayi cikin muryan dake sosarai tace “jinin jikina, ruhina da gangar jikina sun riga sun kamu da tantsagwaran tsantsan kindirmon sonka Baban Amali, naduba gabas kainake gani, naduba yamma kainake gani, naduba arewa kainake gani nakuma duba kudu kainake gani, Baban Amanu kasan da cewa rayuwana tariga tasoma ginuwa akan kifiyoyin tafarfashashen sonka dasuka chaki zuciyana? Ayanzu haka danake maka magana tsokan zuciyana da jinin dake cikinta sun riga sun kulla babban alaka nahar bayan rayuwa da kifiyoyin sonka, ina mai tabbatar maka Ummi bazata rayuba idan babu Noor dinta, Baban Amali da Amanu ina maka tatacchen so da babu ko gudan tsaki acikinsa!” Matseta sosai Nura yayı yanajin sonta na ratsa every bit of him murya chan kasa yace “Ummi koda ace soyayyan daname miki nada tsaki ballema babu, to kalaman nan naki sun tache tsakin tass! Inason Zainabu Abu Hajiya Ummi ikon Allah” murmushi tayi dayaji sautin sosai ajikinshi har yayi calming nata down sannan yasaketa yakama hannunta yace “kınada account kuwa”? Girgizamai kai tayi alamun a’a, yana jinjina kai yace “gobe to idan Allah yakaimu zan kaiki saiki bude akwai tukuicin dazan baki, wannan kukan dakikayi saida tukuici” murmushi tamai tace “godiya nake” yana rike da hannun nata yace “mujeto” binshi tayi suka koma kitchen yace “bye” bye tamai yawuce yafita daga kitchen din Hadiza yağanı a falo ta hade rai amman bai kulata ba yayi sallama da Anty Jams bayan ya ijiyemata raps na kudi already akwai direba dazai kaita airport dan 9 zata fita sannan suka fice Hadiza sai daga murya take sabida Ummi taji, har shagonta Nura yakaita sai dadi takeji tana wani soyewa dashi sabida yan plaza su ganshi tasa yafito yashiga shagonta baxaiyi karya ba business wise Hadiza is good, business nata sai booming yake wlh and he’s really proud of her sake rakoshi tayi ya shiga katon jeep nashi yatafi. Please Ladies stop being sentimental akaratun nan just be neutral, every character in this novel is to teach you something badan kuji bad nayi rubutun nan ba kodan na raba kanku dan group dina yadawo mini arena na fada, gbas gbos everywhere😂 dan Allah kudaina just read, learn and ku gyara gidajen auren ku❤️. Yanzu fa ana zuba kishine anan wato kowa na zuba nashi salon, anyways I am loving this new Hadiza fa😂😂😂 but Ummi ma tarike wuta, I must give it for her resilient nature, the fear na loosing Nuri is there but the gurl keep pushing sai tying all the knots take and I sincerely hope kuna daukan karatun nan. Love you feel free to chat me up if you have anything to say 07012181461. Whatever you do ki tabbatar kin shiga class Dina na MATAN AURE❤️❤️❤️ 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣7️⃣ Bayan Ummi tagama komi takoma dakinta wayanta tadauka tana sake duba lectures da M Shakur tamata na private class da Meena tabiya mata, dalla dalla M Shakur ke mata dan tariga tagaya mata batajin turenci ko kadan, sannan tana iya tambayan matan anything. Zaban abinda zatama Nura yau tayi har Allah Allah take Meena ta iso dan zata taho mata da wasu turaruka daga ZIMS COLLECTION, don Sayan turarukan zims wa.me/+2347039085711 both na wuta dana jiki, dakuma wasu shedanun kayan mata from UMMU FUAD COLLECTION Amana MOM FUAD MAGANA DON SAYAN KAYAN MATA 💃💃💃wa.me/+2348132506044 wanda wai daga kano Meena takira Ummu Fuad tahada mata aka aiko Abuja Meena ta amsa, tana zaune awajen tana bin karatun wayanta yahau ruri ganin Hajiya yasa dasauri ta dauka tace “Assalamu Alaykuma Hajiya ina kwana, kin tashi lpy ya kargın jikinki”? Daga dayan bangaren Hajiya tace “Alhamdulillah yar albarka kinga mijinki surutu yake sani saisa nace gwara nayi magana dake” Dan murmushi Ummi tayi tace “me mahaifiyata keso?” Cikinmuryan dake nuna jin dadin magananta Hajiya na murmusawa tace “Ummi ki gyaramini dakin kasa don Allah bene nan azabane agareni, wlh yo ko daukana Nura zai dingayi yana hawa da sauka dani wannan jim jim jim dinnan har kwakwalwata zani dingaji kinji gyaramin dakinki nada ni nafi sonshi dama” murmushi Ummi tayi tace “yanzun nan zan gyara miki kuma namiki lafiyayyen abinci Hajiya da salak, dan Allah kuzo yanzun nan Hajiya nakosa na ganki” Hajiya na murmushi sosai tace “Allah miki albarka yar nan Nura tashi maza diyata na jirana kaini taganni” Hajiya ta katse wayan, murmushi Ummi tayi ta ijiye wayan ta mike dakin bakın nasama takira mai gadinsu ya tayata suka cire gadon suka maida nan kasa yatayata dauko katifa yakaimata dakin suka hada yatafi, nan da nan tashiga gyara dakin wlh bazaka gane dakinba, yayi kyau tana yi tana mamakin ikon Allah ita datake yar aiki take zama anan yau itace matar mai gida, Allah kenan babu abinda yafi karfin Allah, dare daya Allah kanyi bature. Wucew kitchen tayi tadaura abinci batama idasa gama abincin ba taji zuwansu hijabinta data ijiye nan kitchen ta zumbula da gudunta tafito batai wata wataba ta rungume Hajiya “oyoyoooo Hajiyanaaaa” Sosai Hajiya ke murmusawa tace “ai kya banni na huta yarnan dake da fadawanki su Aisha da Auta tunda gani nazo” sakinta Ummi tayi tadauka har kasa tace “ina kwana Hajiya kunzo lafiya” sosai Hajiya taji dadi tace “tashi tashi Ummi” tashi tayi ta karbi yar purse din dake hannun Hajiya tace “muje ciki Hajiya” Meena takama waist tace “ni baki ganni ba Iyye” Nura yace “inafa zata ganmu Auta taga mamanta mu kinsan bare ne” dasauri Hajiya tace “ku sakinma diyata mara tayi fitsari fa tam, a inda nake awurinta dama ai ku bare ne bakuyi karyaba, muje kinji yar albarka” gwalo Ummi tama Meena da Nura tana murmushi maikyau, Nura yace “nidai natafi tunda baki bukata ta yanzu Hajiya” Hajiya tace “eh tafi din, Allah bada sa’a” Meena ta shiga kwashe akwatinsu daga boot gateman yazo yatayasu suka wuce ciki Nura kuma yatada mota yatafi he’s just happy with Ummi da yanda she’s making his Mom happy and comfortable. Zaunar da Hajiya tayi a falo tazo ta taya Meena sukakai komi dakin Meena tanuna mata wani jaka tamata whispering a kunne. “Muje kitchen kisha” wucewa kitchen tayi saida tafara kawo ma Hajiya ruwa da juice data hada mata sannan takoma kitchen din tasami Meena na kada mata magungunan. Meena tabata wani gora magani na UMMU FUAD COLLECTION tace “sunan wannan sata shakaf” akunyace Ummi ta sunnar dakai Meena tace “dalla matan yayan mu kawai, wannan sunanshi tabanı kaji ruwa, wannan zakije daki kisa tun yanzu sunanshi back to virgin anjima saiki wanke, sunan Yaya Nura sorry yau” akunyace Ummi duk tasha na sakawa ta tafi sama dan saka na sakawa. Wuraren 3 Hadiza tashigo gidan dasu Aman dataje dakanta ta daukosu a school yauwa, Meena da Ummi ne kadai a falo suna kallon wani movie a Netflix a ganin Hadiza yasa duk suka kalleta jin an shigo ba sallama, Ummi tace “sannu da dawowa Anty” Meena tabude hannu tana kallon yaran tace “oyoyooo Amanu and Amalily na” da gudu yaran sukai wajenta suna “Aunt welcome, where’s Hajiya our grandmother” dakin kasa Meena ta nuna musu tace “tana chan dakin kuje ku gaidata” wucewa dakin sukayi da gudu ahankali Hadiza ta ijiye car key duksai taji badadi yanda ko gaisheta Meena batayima gidan saiya mata kaman ba gidanta ba wucewa tayi ko kallonta Meena batayiba itadai Ummi baruwanta tawuce dakin da akace take, sallama tayi chan kasa tashiga dakin Hajiya dake zaune kan carpet da charbi a hannu yaran sun zazzauna ajikinta takalli Hadiza, ahankali Hadiza tace “kuje kucire uniform kudawo Amali” basuyi gardamawa suka tashi suka fice Hadiza tamaida kofan ta rufe tanajin wani iri, she’s feeling super uncomfortable da Hajiya ga nauyinta sai tama rasa mezatace sai murza hannun jakan dake hannunta take, ganin haka yasa cikeda fara’a Hajiya tace “mun sameku lpy Hadiza ya aikin?” Ahankali Hadiza tace “Alhamdulillah Hajiya” suka sake shiru, Hajiya tace “ga waje ki zauna” girgixa kai tayi tace “a’a basaina zaunaba zanje sama nayi wanka ne” tayi shiru batare data fitan ba, yanda zata bada hakuri yana mata nauyi da wahala abaki saikuma chan still tana a tsayen daga wajen kofa tadaure da kyar tace “ahhh Hajiya kiyakuri” murmushi irin na manya Hajiya tayi tace “bakomi Hadiza ai yariga yawuce, jekiyi wanka abinki kifito kici abinci” Gyadamata Kai Hadiza tayi tajuya dasauri kaman ana turata tafice batare data kalli falon ba tawuce sama ta shige dakinta, Hajiya ta girgiza kai kawai yanda Hadiza bata gaidata ba yatabata but batason abin ya tsayamata arai hakan yasa ta zubar tacigaba da kan charbi abinta. Har akai İshak bata fitoba tanajin hiransu da muryan su Amali akasa but bata fitowa, kawai she don’t feel belong ne at all, bayan magrib Nura yashigo gidan Hajiya tace “kirawo Hadiza muyi dinner” baiyi musuba yaje sama bude dakinta yayi tana zaune tana aiki da laptop yace “sauko muje muyi dinner, Hajiya tace nazo nakiraki” yatsine fuska Hadiza tayi tace “nariga naci abinci basai na saukoba” tsayawa yayi yana kallonta kafin yahade rai yace “sauka muje” wani kallo tamai kaman ta baro bakan magana ta gayamai tadai daure tayi shiru ta danne tace “please Nuri nayi dinner nagaya maka, over feeding kakeso nayi or is it by force mutum yaci abinci?”? Kallon fuskanta yake ganin she’s in that her not so good mood yasa yace “suit yourself” yajuya yawuce yatafi tabishi da mugun kallo tace “tunda masu zugaka sunzo ai daman dole kayi haka, all along i was right daga zuwansu last time ka chanza sukasa ka auromin yar aiki, ai wlh da mahaifiyarka da Meena bazan taba yafemusu ba nothing can ever make me like this those humans da Ummi, I can never mtswwww” taja tsaki wound na heart nata nadawowa sabo, wayanta Hadiza ta dauka tasauka dagakan gadon tana dialing number Anty Jams tawuce kofa tayi locking kofan da key daidai Anty Jams ta dauka tawuce bayi zama tayi kan matsan dayake arufe cikin sanyin murya tace “Anty Jams Hajiya takara dawowa gidan” jin muryanta yasa Anty Jams tace “saikuma akayi yaya dan Hajiya tazo”? Shiru Hadiza tayi tana lumshe idanu kafin chan tace “Anty Jams bawai i hate Hajiya bane but I hate living da ita at the same space Anty Jams, akwai wani vibe da energy danake getting from Nura idan yana tareda maman shi kaman irin baya bukatana dinnan am noting, yanzun nan danace bazanyi dinner ba bai damuba yayi tafiyanshi da dane daya lallasheni na yarda nabishi, he feels stronger idan Mamanshi na gidan nan, remember duk abinda nakeyi baya komi but the last time datazo ai sabida ita yasakeni yakoreni ban kwana agidana ba, Anty Ja……” takasa maganan ta hanyar rufe bakinta datayı jin kuka yazo mata Anty Jams tace “ina jinki” deep breath tayi taking tace “I feel suffocated idan Hajiya na gidan nan the atmosphere is toxic for me kaman inta kurma ihu, nasan yanzu datazo she’s cooking something ne so ake ahademini kai da Hajiyan da Ummi da Meena harda babban munafukin Nura da saiyau dasafe yake sanardani zata dawo gidanmu, Anty Jams from abinda nake gani Hajiya is not even ready to leave my house for me, yanzu haka zanta zama da Mamanshi agidan nan? Ina sharing gıdana with my mother Inlaw? Ita lokacin datai aure haka tayi zama da surukanta? Fisabillillahi kinzo kin wani tare gidan yaro sabida kawai ahanani sakat, ko Allah yasan fadan dakikamin yasa bance komiba to amman Allah yasan i hate her staying agidana wlh and Allah ma yasan ba lallai na iya keeping up da wannan pretense dinba dan nasan munafinci tazo tayi da sunan ciwon karya” “Hadiza! Hadiza! Hadiza!!” Anty Jams takirata sau uku tace “Hadiza kinji sau uku nakiraki ko”? Hadiza tace “uhm” Anty Jams tace “Hadiza wlh nagaji da unnecessary complains dinki tell me tunda kuke Hajiya tataba miki wani abu”? Ahankali Hadiza tace “directly no but indirectly ai ita tasa aka sakeni, tana cikin gidan tana ganin komi, kuma ita takira Nura yadawo ta surfafamai karya akan fadana da Meena da baima tsaya yaji tabakina ba yasakeni dan haka yes tamin laifi” wani dan murmushi Anty Jams tayi maidan sauti tace “let’s assume Hajiya cema tasa askeki which zan iya ransuwa ba itabace, idanma itace ai ta isane, tana matar data tsugunna ta haifo mijin dakika aure, build this Nura of today that’s so gently and sweet ki dauko mata police bazata ce asakeki ba yo konine zance ai ballema ba itabace” cikin korafi kaman zata fashe da kuka Hadiza tace “nidai ko ba itabace ta tattara ta barmin gidana i hate her staying in my house Anty Jams wlh babu wani ciwon datake bakinta rass the whole treatment yakawota nan Abuja is just a strategy ni kawai ta barmin gidana, banason zama da ita, I hate staying with her, spirit dina baison zama aduk inda take i called you ne nake gayamiki sabida ki bani better way dazan fada wa Nura yasa mamanshi tabar gidan nan dan banso namai magana yaga kaman na tsaneta ne” “kaico!” Anty Jams tafadi asanyaye tace “Hadiza on a serious note yaushe kika dawo mara imanı haka? Hadiza a known diabetic patient, hypertensive patient kike cewa lafiyan ta kalau? Hadiza old age kadai cutane, old woman dakeda yaron shekara kusan hamsin kike cewa lafiyanta kalau ciwonta karyane and is strategy? Must one be in coma kafin ki yarda that person is sick? Ohh Innalillahi” Hadiza tace “Anty Jams kona miki karya bazanma Allah ba, ni kawai na tsani Maman Mijina Hajiya agidan nan shine kawai maganan, har cikin raina wlh na tsani ganinta acıkın gıdana, I hate staying with her I can’t stand her sight” Iska Anty Jams ta fuzar azafafe cus tafara gajiya tace “Hadiza kinga Allah yasani nabaki duka shawaran dayakamata nabaki, amatsayina na yayanki na sauke hakkinki dake kaina na nuna miki gaskiya nakuma nunamiki kuskuren ki tunda kinki ji kije kiyi DUK ABINDA KIKAGA DAMA yes I said it duk abinda kikaga dama kiyi, do things your way ke kika sani but kisani duk tsuntsun dayaja ruwa shi ruwa zaija” azafafe Hadiza tace “baki kikemin Anty Jams daga nagaya miki matsalata? Kin bani shawara naji nabi I am still managing, wait ma Anty Jams da ace ina abu my way da yanzu wlh na hurama Nura wuta a tsuliya nasa ya saketa itama yarinyar na korata kauyensu danshi kanshi Nura knows how stubborn i am, but still na saurareki sabida kar yazamto ban saurari shawaran yar uwata ba, Anty Jams barikiji u can ask liman Mata daban uwarmiji daban, kowacce tanada hakkı kan mijinta, I have hakki akan mijina which dole ya sauke itama Hajiya haka, I know he’s trying taga good doctor agarin nan must he bring her to my house eh?? Nura ya gina estate daban daban agarin nan bai rasa gida sabo fil dazai saka mamanshi da kanwarsa ba why my house eh? Kawai anzo an dauramin jaraba ga mata makira taitayin maka faram faram afuska buts she’s a devil in disguise” dasauri Anty Jams tace “A’uzubillahi Hadiza, how will you feel idan Matan Aman takira ki Makira devil”? Dasauri cikin tsiwa tace “wow Anty Jams kin karamin baki kuma well bari nabaki amsa bazan taba da girmana da tsufana natashi naje natare agidan Aman ba natakuramai da matar shi nahanasu sakat wlh bazan tabayiba ko da ko am on my deathbed” murmushi Anty Jams tayi tace “babu ta yanda rayuwa bata kasancewa just pray, itama Hajiyan ba ason ranta take gidanki ba, tunda kukai aire ta taba takowa gidan ki banda yanzu” cikin dan ihu Hadiza tace “wat are you saying Anty Jams? Don’t forget matan nan nada yara mata guda uku dasukai aure maisa bataje wajensu ba su mata ai sunfi dadi zama da iya kula da mamansu sai gidan danta namiji zatazo, bayan Aisha na Egypt, Egypt ma da akwai manyan hospital inda zataje taga specialist, banda sauran yaranta dake nan Nigeria nagaya miki duk makirci ne and well executed plans gashinan ai daga zuwa ta na farko sunsa an sakeni suka zugashi ya auremin yar aiki how can I love her? Taya zan dinga zama da irin matan nan bayan ta cutardani? Wlh I hate her, I hate all family Nura, i hate them with passion sabida duk dasa hannunsu Nura yamin abinda yamin, da inada wani iko dasaina rabashi dasu wlh Muga karyan tsiya mugaye kawai kuma sai Allah yasakamin” Anty Jams tace “kinga saida safe nagaji dajin haukanki” cikeda bakinciki Hadiza tace “eh saida safe from now on I will be doing things my way and watch zakiga yanda zan gyara komi wlh in no time, bazan Kara daukan shawaranki ba dan it’s sucks, kissa da kisisina to hell with it I can’t pretend and I will never pretend because of a man if I hate you I hate you if I like you I like you that’s Hadiza, bazan kara kiranki for my issues ba saida safe” ta katse wayan Anty Jams na kokarin magana ta tashi ta kunna tap na washhand basin ta wa ke fuskanta tana kallon madubi tana fusar da iska kirjinta yamata nauyi sosai she feels alone. *** Ganin yanda suke kallonshi ganin ya sauko shi kadai yasa yace “tayi bacci Hajiya nasan gajiya tayi” Hajiya tace “ayyahh” nan sukahau cin abinci Ummi ke feeding Aman da Amal as usually abincin yayi dadi suna gamawa Nura yatashi dan zuwa masallaci Hajiya tace “Meena ke ki tattara wajen ki gyara, ke Ummi tafi sama ki kimtsa kin shiga kitchen ki wanka kihuta yau mijinki na dakinki saida safe” akunyace Ummi tace “Hajiya kidan bari na kamama Meena aikin dan Allah” “kul bar Meena tayi, tafi nace” akunyace tace “to saida safe Hajiya saida safe Meena” murmushi Hajiya tayi tace “Allah miki albarka Ummi, su Amanu zasu tayani hira ko” atare yaran sukace “eh grandmom” Ummi tace “bazaku bini ba” Amal tace “Anty Ummi grandma zata mata tsutsuniya” aka kwashe da dariya dasauri Aman yace “is tatsuniya” Hajiya takalli Ummi dake dariya tace “wuce kitafi” wucewa Ummi tayi. Ummi na shiga dakinta bayi tafada lafiyayyen wanka tayi tai brush wlh yau she’s super happy yana wajenta ita kanta mamaki take yanda takejin son Nura yanzu, fitowa tayi ta zauna gaban madubi ta shafamai sannan tadauki turaren da Meena tasaya mata daga ZIMS SECRET mai suna soul unravel tabude wowwww saida ta lumshe ido saitaji kaman ma ashe duka turarukan datake amfani dashi ba turare bane kamshi is soo cool and sexy, irin kamshin nan ne that’s tantalizing kaji kaman zakaci haka kamshin yake shafawa tayi a hannunta ta goga abayan kunne, saman kirji dakuma kasan nono Ya Allah! Dakin kaman anyi barin turare, tashi tayi taciro wani crazy lingerie daga HABISMA UNDERWEARS red ne color tashiga sawa Ummi data kalli kanta amadubi saida ta kulle idanunta dagudu tace “Innalillahi jibeni kaman yar iska” rigan nada nipple holes so nippi nata na waje while sauran jikinta na cikin transparent rigan dasauri tace “M Shakur maisa kikace irin kayan yan iskan nan ake sama miji saikuma tayi shiru ta sake juyawa ta kalli kanta wannan shine mini tsirara, murmushi tayi ahankali tace “amman kuma ko a yan iskan ni kyakkyawace kaman bani ba” murmushi tayi ta lumshe idanu tana tunani takosa Baban Amali yazo suyi, this two days da ba’a taba jikinta ba duk taji batajin dadin komi, Baban Amali daban ne wlh yafi Mudi iya komi, Mudi bataso ya nemeta lokacin nan amman ayanda takejin Dadyn Amali da yau bazai nemeta ba halan saitai kuka, gashi ya iya cin wajen cin kashi yake mata bacin namaba dan wlh gwaguya ne wannan ba tauna ba abinda yakema wajen😂 Sake daukan wani turaren wuta tayi shima daga zims mai suna MAGHRIBEE tajona burner tadaura akai dakin yafara mashahurin kamshi, irin kamshin nan dake maida daki so cozy kaji sha’awa takamaka takalli gadonsu tsaf tsaf tana kallon Aveeno baby oil dake gefen gadon tai wani shegen murmushi tace “Allah yasa na iya Nura massage din da M Shakur takoyamana a class” dasauri tace “ai Nuru, Nuru, Nuru bansan Mesa nake cewa Nura massage ba kodan yayi kama da sunan mijina ne” sake kara feffesa turare tayi ta zare ribbon din gashinta tasaki gashin ta taje gashinta baida tsawo kaman na Hadiza but is soo fine and silky gashi ba baki bane gashin agwai gareta ja brown, kallon agogo tayi ganin almost 9:30 taşan yarığa yadawo yanadai wajen Hajiya ne yasa tawuce bayi tashiga tara ruwa a bath tube saida ta cika, batasan yanda ake hada bubble bath ba but tundadai kumfa akeso ruwan yayı yasa ta dauko shower cream nata da Nura ya sayamata na Olay tadinga matsawa a ruwan gashi da dan banzan kamshi ta zuba hannunta cikin ruwan tashiga kadawa abin saiya zamanmata kaman wasa saita fara dariya ita kadai abayi kana ganinta kasan she’s so happy and excited mijinta zai kwana dakinta yau saida ruwan ya kumfe ta tashi ta wa ke hannunta a pampo taja kofa tafito tazauna tananan zaune taji Nura yazo sama yaje ya kwantar da Aman datayı bacci yasake komawa kasa yadauko Amal itama yakaita dakinta sannan ya tsaya gaban dakin Hadiza ya murza kofan yaji arufe knocking yayi na kusan 3min amman bata budeba yasan Hadiza na bacci dawuri sabida gajiya daga aiki but yanda yadade yana knocking yasan dole zataji barinta yayi ya kashe wutan nan falon saman sannan yabude dakin Ummi da sallama dük yanda Ummi taso ta daure tarike kanta wlh takasa, da gudu ta taso tai wani tsalle tafada jikinshi kaman yar biri alalo alalo ta rungume shi tace “oyoyooo Nisful Hayati, Ahlan Wa Sahlan Marhabanbika Ya Zauji” washe baki Nura yayı yatareta da hannu daya yasa dayan hannun yatura kofa yana saka key yana murzawa yace “yau mun koma labarawa, haka akai kewana anan gidan” cikeda murna tana kara kwakumeshi kaman fa wacce tai shekara dari uku bata ganshi ba tace “anyi kewanka agidan nan kaman ba gobe” “Ummi u smell damn down goodddddd Ya Ilahal Al’ameen, wowww! Wani turare ne wannan Ummi kikasa? Bantabajin kalan kamshin nan ajikinki ba” Yay maganan yana dagota yana mammanna fuskanshi awuyanta kaman zaici wuyan, rungume kanshi tayi tana kallonshi adan shagwabe tana abu kaman wata little baby tace “Meena tasaya mini turaruka daga ZIMS COLLECTION” dasauri Nura yace “wowww, wanda kuma yake kamshi adakin fa duk nata ne naji ba irin kamshin wanda kika saba kunnawa agidan da ba”? Gyadamai kai tayi yace “wowww zan baki kudi keda Meena ku suyo every turarenta na gida dana jiki idan tanada na maza ma inaso kinji yanda kike kamshi ne I love good kamshi Ummi ashhh” ya manna kanshi awuyanta yana kallon nipples nata dake waje kawai yakai bakinshi dasauri Ummi ta fizge kanta tace “ashhh” dan dariya yayi yana lashe lips kaman bakin maye yabi rigan da kallo babu abu na jikinta dabaya gani batasa komi aciki ba kawai mikewa yayi wani murmushi Ummi tayi tawuce hanyar bayi tana shaking ass tace “zokai wanka nahada maka ruwa, rigan baccin shima duk aikin Meena ne from HAIBISMA” tabude bayın ta shige dan ijiyan zuciya yasauke yashiga cire kayanshi anan wajen kofa ya barsu yatafi bayın empty yana bude kofa Ummi take tsaye gaban bathub din tasa hannu tana duba zafin ruwan tajuyo ganinshi ba kaya yasa tarufe idanunta tace “wayyoo ciji” dariya Nura yayı yazo gaban bathub din yace “zokima cijin naki wanka” yafada cikin bathub din ya fizgota ciki ihuu Ummi tayi tana bude idanunta tace “nayi wanka fa ni” hannunshi yasa yana kama riganta yana kokarin cirewa yace “wannan daban ne danaki dan mijinki ne zai miki” ita wlh duk batasan abubuwan nan ba amman abin dadi yakemata cire mata rigan yayı ya jefar yana kallonta yakai fuskanshi saitin nata yace “me kike boyemin boobs a kumfa” lips dinta Ummi talashe tana kallon pink lips dinshi yanda suke motsi yana gabana, awani irin hankali yatura yatsunshi cikin gashinta yana bata light head massage dayasa take lumshe idanu tana budewa tana kallon lips nashi yace “kinason kisha bakina”? Gyadamai kai tayi murya chan kasa tace “eh nayi kewan sumbatar ka wlh” kankamcewa idanun Nura sukayi yace “tsotsi na kasan banda na saman” kaman jira Ummi take hannuwanta takai ta daura kan kuncinshi lumshe idanu Nura yayı sabida wani dumi dayaji na danshin ruwan zafi da hannun Ummi keciki takai bakinta taja lips nashi na kasa sai kawai taja duka lips din murmushi yayi yasata ajikinshi sosai Ummi loves kissing him is just one of her fevorite thing to do ya lura bakinshi is just like wani adventure for her har wajen delun shi take exploring, the way her nipples were scratching his chest jiyake kaman yayi bending nata aruwan kumfan nan ya soka mata the sokable ya daina yayı squeezing boobs nata ganin suna nema su manya nay. Su manta bayi suke yasa Nura ya dagata yadauketa suka tafi wajen shower ya kunna musu ruwan zafi ya dauraye jikinsu mannata abango yayi zai shiga ahankali Ummi tace “Baban Amali” tsayawa Nura yayı yakalleta ahankali da muryanshi da baya fita sosai yace “naam” murmushi tamai cikeda kunya dan bazata iya kallon idanunshi tafadi ba ta manna kanta akirjinshi tana kulle idanu tace “zaka iya bani kanka yau ka barni nayi yanda nakeso dakai”? Wani kalan dariya Nura yayi yace “yihuhu” saikuma ya cije lips nashi yana kallon kanta kafin yasaki lips din yace “nabaki Ummi kiyi yanda kikaga dama dani like your little boy kawai ki bada uwarni Nura zaibi” murmushi tayi tafito daga jikinshi tareda juyamai baya tace “katafi gado ahaka kayi ruf da ciki gani nan zuwa” babu gardama ko tambaya kaman wanda Ummi tama magani yace “angama Babyna” juyawa yayi yafice yaje straight to bed ya kwanta ruf da ciki, murmushi Ummi tayi ahankali tace “Allah yasa yaji dadin abin da zanmai” sannan tafito daga bayin tareda rufe kofa, kashe wutan dakin tayi tarage sanyin AÇ ta taho zuwa gaban gadon ta kunna side lamp zuwa blue light dakin yayi wani dim blue light mara haske sosai but u can see mutum, oil din nan ta dauka tabude tsiyayawa tayi nasha nasha tundaga wuyanta yana gangara har cinyanta kafin tasa hannu ta shafa ako’ina ajikinta kaman wacce aka tsamo daga kogin oil, gently tahau saman gadon ta zuzzuba a bayan Nura tundaga bayan wuya har zuwa ass da kafa tadaura hannunta ahankali saman bayanshi Nura yace “uhmmm” murmushi Ummi tayi tashiga shafawa tace “tun yanzu kafara nishi Mijina, nishi sai anjima, tausa zan maka na cire gajiya daga jiki da damuwa, sannan zai kara maka lafiya” cikin murya irin na wanda yakai kokolula din nan yace “afara yi duk yanda kikaga dama da ni Ummi komi dakenan nakine” tass ta gama mulke man ta ijiye sannan tahau kan jikinshi tazauna saman ass nashi smooth Vijay nata ya mannu da ass nashi wani malalacin kara yasaki yace “hmmmm” awani irin hankali slowly Ummi ta kwanta abayanshi fuskanta na wuyanshi jikinta na bayanshi kafafunta na kan nashi tayi wani tafiyan tsusa ajikinshi da tafiyan dodon kodi jikake wani zuuuut sabida oil. Nura yace “Ya Allahu Ya Quddusss, Umm….” Gille spinal cord nashi tayi da boobs dinta dasukaji oil Nura yace “wayy….yoohoyooo” yawani kifo da ita yajuyo yace “Ummi zaki kasheni wannan ai saina kawoma katifa bakeba, wai zan haukace fa saura ki…….” dasauri Ummi ta taso yatsanta takai kan lips nashi like a bitch authoritatively tace “kwanta” wlh kaman Aman komawa yayi ya kwanta yana kallonta, gabanshi ta kalla daya mike sambal yana har bawa yana nishi kaman zai tsalle ya shige jikin Ummi kana gani kasan yakosa yasami abinci sai kallon Ummi yake da jikinta ke kyalli tasa hannu ta dauko oil din ta diddiga akan joystick din ta ijiye oil din kafin ahankali takai hannunta biyu tasa J din atsakiya ta hade hannayen tawani zuge joystick din dayaji oil da hannunta kaman ana zuge hanjin ragon layya jikake wani zuuuuuuiiiit. “Jar uban chan…….” Nura yasaki wani babakeren ihu yace “wayyooo g*nd*na!” Dan senses nashi yatafi tasss……. Karna tsumaku da yawa mu tsaya anan makesure kuma kun sayi turaruka from ZIMS COLLECTION ta hanyar clicking on this link wa.me/+2347039085711 Number :07039085711 Link:wa.me/+2347039085711 Brief description: today I am preaching to those who are in between the two… You don’t know what your taste of preference is as an incense lover.. Baki san ko kamshin zamani kike so ko na gargajiya kike so ba.. Idan Nache kamshin gargajiya wato ki kona turare kiji yana kamshi mai dadi kuma zakiji kamshin icchen da kike konawa ba tareda yayi kauri ba kuma wannan kamshin yayita kama guri sosai. Ba wai kin kona yanzu anjima kin nemi kamshin kin rasa ba 😞 ba abunda yafi haushi ache kin siya turare da tsada sannan ki kona ki nemi kamshin ki rasa automatically kin kona kudinki ba tareda kwalliya ta biya kudin sabulu ba. Garzaya instagram @zims_collections kuji abunda ake ji. Amana MOM FUAD MAGANA DON SAYAN KAYAN MATA 💃💃💃wa.me/+2348132506044 💫 MATAN KO MAZAN 💫 ✍🏻M SHAKUR IRSHAAD TIGERNUTMIX gidane na harkan sarafaffen garin kunun aya, all you have to do is add water🥰 Chat them up and order for your idan bakison dogon aiki İrina and thank me later wa.me/+2348067231876 https://instagram.com/irshaad_tigernutmixnmore?igshid=OGQ5ZDc2ODk2ZA== EPISODE 1️⃣8️⃣ Tunda Nura yafara knocking kofan Hadiza take jinshi bawai taki budewa bane sabida batason taganshi ba, kawai taki budewa ne dan batasan yanda zuciyanta zaiyi accepting sallaman dayazo yamata zaije dakin yar aikinta ya kwana bane ba, yanzu dagasken gaske dai yanzu Nurin tane zaije ya kwana da wata a matsayin matanshi? Bata taba sanın a day like this zaizo arayuwanta ba, wani kumfan bakın ciki ke tasomata daga zuciya yanzu Ummi wannan, yar aikinta ne ta aure mata miji? Yau itane mijinta yafita daga dakinta yakoma dakin mai mata aiki a matsayin matarsa? Ta tambayi kanta tana kara juyawa tana kallo dayan side na bed dan takasa bacci, ijiyan zuciya tasauke ta danne duk kalan kukan bakın cikin datakeji, yanzu duka abinda Nuri ke mata haka zai dingama yar aikinta? The way tasan nakedness din mijinta haka Ummi ma zata sani yanzu? Yanda ya iya kwanciya da macen nan haka zaije yama Ummi ma? Hasbunallah! Tafadi tana tashi zaune tana taba zuciyanta is as if all this while da duk take haukanta dajin zafi da ciwo na ya auro Ummi bakomi bane cus duka lokacin adakinta yake kuma kullum cikin lallashinta da nunamata so yake yaune reality na tsantsan bakın ciki ke zuwanmata ganin fa da gaske yanzu Nuri yayi wani aure kuma Ummi yar aikinta ya aura yanzu haka yana dakinta mema sukeyi? Ta tambayi kanta kaman mahaukaciya tana zabura ta sauko daga gadon. Tace “the way Nuri make love dani this two days haka zaije yayi da yar aikina itama? Ya kwanta da ita kaman yanda yake kwanciya dani?” Tayi maganan tana tafiya wajen kofa completely out of her senses, tashiga murza key tabude kofan ahankali daidai tasa kafanta daya tafito taji tashin Ihun Nuri dawata murya da ita kanta batasanshi da itaba dan muryan wanda baya cikin tsantsan hankalinshi ne. “Wayyoooo g*nd*na!” Chak Hadiza ta tsaya takasa karasa fito da second leg din waje sannan takasa maida leg din da tafito dashi ciki she was just there. Yanda Ummi ke tazuge da joystick din Nura yana ihu sai kawai ga hawayen tsantsan dadi nafitowa daga gefen idanunshi yana wani bankarewa yana nishi kaman zai haihu yace “Ummi zan mutuuuu, u are killing me baby, Babyna kinfi duka matan duniya iya sarrafa miji, Ya Rabbi Ya Allahuuuuu Umm……” Ashe maza na vibrating yanda Nura yahau vibrating kaman zai mutun da gaske yana bucking up dasauri Ummi tasake joystick din wani kalan fizgota yayi kawai yafada kanta still vibrating trying to slid in yakasa kawai dagashi har ita suka zare daya shige he just went absolutely crazy the hitting and knacking was just too rigorous, none of them ke hayyacinsu dan infact today’s sex was the best sex in his entire life baitabajin dadin dayaji yauba kodan Ummi romancing nashi ne ohooo. Taushe baki Hadiza tayi tana ganin duhu duhu sabida yanda takejin muryan mijinta kaman yanacin gindin zinare ba g*nd*n mace ba, she could hear the intense stroke dayake watsama Ummi extremely fast, tanajin squeaking na gadonsu, she could hear muryan Ummi kasa kasa tana nishi kaman mai nakuda, sai a lokacin karfi ya shiga jikinta taja kafanta ta maida daki tawani kalan bugo kofanta kaman zata cire gidan taduke anan gaban kofan ta taushe bakinta tana kuka, ta dauka yanda ta buga kofan zaisa su daina ko Nuri yafito yazo wajenta da sauri but is as if bama suji karan kofan ba duk uban karan dayayi wannan karan kaman ma kuka taji Nuri nayi ma yanzu, da gudu Hadiza ta tashi tafada kan gado tadauki filo biyu ko wanne ta taushe kunnen ta tana wani kalan kuka da bata tabajin tayi irinshi in her life ba, mijinta ke ihu akan yar aiki ta haka yana kuka da uban ubanme Ummi tafita? Wlh babu wani abu na diya mace da bazata nunama Ummi ba, kyau, gashi, farin fata, diri, gaba da baya, ga tsafta, and wlh yayi karya yace batada dadi cus tana spending kudinta taje spa tayi su vijay streaming, rejuvenating infact har O-shot tatabayi sau daya Nuri kuma enjoyed the sex danhar saida yayi magana lokacin but still Nuri bai taba mata haka ba, infact Nurin datasani is not even much of a talker idan suna sex breath nashine kawai ke chanzawa zataga yana numfashi dasauri while is heart is racing but magana gurnani ihu batasan Nuri dashi ba, what is he doing akan yarinyar nan? Akwai kalan styles dabata bari yayi da itaba? Baitaba cin mace bane ko me? Ita dusa ne da baitaba all this moans and cry akanta ba sai akan wannan gidahuman yar kauyen” ihuuu Hadiza takarayi mai karfi tace “Nura I hate you, na tsaneka na tsaneka for hurting me this much, I hate you Nura” tafashe da kuka tana cire filon dake kunne ta tana jefarwa kaman dasu take fada tace “I hate you Ummi I wish you the worst and the most painful death aduniyan nan, for coming into my life, for yaudarata dacin amanata, for causing me pain, for auren mijina dakikayi, Allah ya wulakantaki yakuma kashe ki Ummi mutuwan wulakanci ahhhh wayyooo zuciyata” Hadiza tai nishi tana fuzarda iska kafin tayi rarrafe tashiga bayi kawai ta zauna akasan bayi kan tiles, da kyar ta iya mom hannu ta kunna shower na ruwan sanyi yana fadowa kanta ta kankame kanta tana wani irin kuka mai tsuma rai, auren Ummi da Nuri yayi hurt her a lot, but yau wani special kind of inner hurting takeji she can’t even exaplain sabida yanda taji yana kuka akan Ummi, mesa Allah yace maza suyi mata hudu?? Ta tambayi kanta, cikin kuka tace “Ya Allah bawai ina challenging umarnin ka bane but amma Ya Allah I’m hurt, nakuma san kafadi cewa baka jarabtan bawanka da abinda yafi karfinshi but Ya Allah wannan jarabawan dakakemin kaman yafi karfina, Ya Allah ka sassauta mini, Ya Allah ka sausautamin Ya Allah zan mutu fa, zuciyana namin zafi, kaina namin zafi, jikina namin zafi komi namin zafi, mesa zaka dauramin soyayyan wanda ya yaudareni haka yaci amanata? Nuri yamin the worst thing Mesa bazan tsaneshi ba na tambayeshi saki nayi gaba na barmai gidanshi da yar aikina why of all time yanzun ne nafi sonshi sama da da ma? Mesa yanzu ne nakema Nuri wani kalan so dakoda muna saurayi da budurwa banjin namai kalan so din nan ba? Ya Allah why wani laifi namaka so big that u are punishing me da abu guda biyu kuma mafi zafi arayuwa, soyayya da kishiya? Eh”? Hadiza tafashe da kuka tama manta cikin bayi take sunayen Allah kawai take kira, cikin kuka sosai tahade hannunta biyu 🙏 tace “Ya Allah jarabawan nan yamin tsauri, Ya Allah kaine Al Gaffar mai yafiya, kuma Arraheem mai jinkai, Ya Allah kaine kuma Al mutasariffu mai jujjuya al’amura Ya Allah ka gafartamin kurakuran dana maka, Ya Allah ka jinkaina Ya Allah ka kuma juyamin lamurran nan nawa, Ya Allah I hate feeling this way kozanma kowa karya bazan iya makaba cus kana ganin zuciyata, Ya Allah gani nake kowa yajuyamin baya kaima kuma kajuyamin baya! Ya Allah nasan fushi kake dani, Ya Allah ka kalleni I’m not okay, ka sausautamin, ka rangwantamin kakuma yassaremini wayyooo zuciyana” kawai ta kwanta flat akasan tiles na bayinta ruwa na dukanta kaman ba Hadiza mai tsafta ba tana kuka mai taba ruhi. Sai wajajen 3 Nura yadawo hayyacinshi tuni Ummi tayi bacci dan itama taci uwar wahala a hannunsa, gently yajaye jikinshi yamike tsaye ahankali yawuce bayi wanka yahauyi yana murmushi remembering all that went down chak ya tsaya dan yanzu ne yanda yayi ihu yafice hayyacinsa na dawomai, wani kalan rashin dadi yaji deep down yana addu’a Allah yasa batajisu ba dan dagashi har Ummi were soo crazy and rough sabida sunyi kewan juna, ijiyan zuciya yasauke yakarasa wanka yafito ya shirya cikin jallabiya yawuce ahankali yabude kofa yafice gudun karya tada Ummi hanyar dakin Hadiza yayi yadade a tsaye sannan yasa hannu ya murza kofan jin kofan abude yasa ya tabbatar Hadiza tafito dan dazu ai kofan a kulle, bude kofan yayi yashiga ciki yabi filolin daya gani akasa da kallo yana kallon gadon dabata akai jin saukan ruwa yasa yakalli bayi hango kafafun Hadiza yayi akwance akasan bayin da kofan bai gama rufuwaba yasa yaji gabanshi yafadi sosai da gudu yayi bayin yabude kofan bayin da kyau ganin Hadiza kwance a sheme cikin bayi ruwan shower na dukanta with full force idanunta a rufe dan kaman ma bata numfashi dan ruwa na sauka kanta bata motsi yasa da gudu yayi wajen ya tsugunna yadagota yace “Hadiza!” Yanda yadagota haka ta taso sharab tabiyoshi wani kalan mahaukacin fadi gaban Nura yayi yakai hannunshi dake rawa sosai ya shiga bubbuga kumatunta yace “Hadizaaa Hadizaaa!!” Wlh ko motsi, hannunshi yakai da sauri yakama hannunta at the same time yakai dayan hannunshi yana kashe shower, murza tsakiyan hannunta yayi still she’s not moving dasauri ya kwantar da ita yace “no no noooo Hadiza kada kimin haka! Hadiza” dukawa yayi yabude bakinta yadaura nashi yabata iska yadago yashiga bata CPR kusan 6min yayi but no sign of pulse ko heart beat, ahaukace Nura yadagota yawani jijjigata da karfin gaske yace “Hadizaaaaa!” Falling hannunwanta sukayi sharappp alamun babu rai ajikinta!!!! INNALILLAHI WA INNAILAIHI RAJI’UN!! HAKIKA KULLU NAFSIN ZA’IKATUL MAUT, THUMMA ILAINA TURJA’UN. Saikun jini ranan ASABAR!!! 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 1️⃣9️⃣ OYA KU GARZAYA KUJE KUSAYI KAYAN BACCI DAGA WACCE TAKE SUPPLYING UMMI💃 We adorn your inner beauty👙 Make you confident & comfortable with our unique Underwears ranging from; Panties(full cotton&lace,spandex pants, thongs, g-strings...) Jeans, cotton tops, cotton Italian gowns and more Bras(padded&non padded, wired&wireless, strapless...) Sleep/indoor wears(silk, cotton, satin & lace) & more! https://chat.whatsapp.com/FICkwWmt8xqLuzWi1aTVQe 08034145600 19 Ihun da Nura yayi saida yatada kowa na gidan. Azabure Ummi tabude ido ta tashi zaune da sauri tashiga waige waige ganin Nura baya dakin, jin ihunshi for the second time yasa dawani kalan sauri ta diro daga gadon dan tasan ba lafiya ta nemi hijabinta har kasa tasaka dan ba kaya ajikinta tafito da sauri daidai Nura nafitowa daga dakin Hadiza da jallabiyanshi ajike dauke da Hadiza da kayan bacci ne kawai ajikinta komi na jikinta diddiga yake da ruwa a sheme hannuwanta na lilo daidai lokacin Meena itama na haurowa saman Aman da Amal duk sun bude kofa sun fito, mugun faduwa gaban Ummi yayi daga ita har Meena atare sukace “meya faru”? Nura baimabi takansu ba yashiga sauka kasa Amal tafashe da kuka cikin magagin bacci tana sosa ido dasauri Ummi ta dauketa tana kama hannun Aman dayace “what happen to Mom”? Bata iya bashi amsa ba takamashi sukai kasa da Hajiya Nura yaci karo dake tsaye gaban bene ganin Hadiza a hannun Nura kaman jaririn da aka haifo daga ciki yasa tace “Subhanallahi meke faruwa”? Arude Nura yace “Hajiya bansaniba abayi na sameta ahaka, dubamin ita Hajiya bata numfashi, Hajiya dubamin ita” dukawa Nura yayi rikeda Hadiza awajen dasauri Hajiya ta duka takai yatsanta kasan hancin Hadiza but shiru, saikuma dasauri tasaka karamin yatsanta cikin kunnenta takai babban yatsanta wajen sajenta tayi shiru saikuma tacire dasauri takai hannunta damanta idanunta tabude duk Nura nabin mamanshi da kallo dan Hajiya ita kewa mata dasuka rasu wanka a unguwansu akano. Ganin yanayin idanunta yasa Hajiya tace “Innalillahi Wa Innailaihi Raji’un!” Dawani kalan sauri Nura daya gama rudewa yace “noooooo! Hadiza this is not our promise Hadiza, Hadiza” dasauri Ummi tajuya dasu Aman da Amal dake kuka sukai sama baikamata yara na ganin irin wannan abunba, Meena ta taushe bakinta jikinta na rawa, hannunshi Nura yakai yana bubbuga kuncinta yace “Hadiza wake up, wake up don’t do this to me Hadiza, don’t do this to me!” Yayi ihu yana jijjigata ajikinshi yace “tayaya kikeso na raini Aman and Amal ni kadai on my own without you? Don’t betray me this way, I want to spend all my life dake Hadiza kitashi ban yarda ba, wake up” ya dinga jijjigata kaman zai karya mata wuya dasauri Hajiya takama hannunshi tareda girgizamai kai tace “Nura!” Ihu yayi yace “Hajiya nooooo, tasan alkawarin mu, she can’t leave me so soon, a……..asibiti…” kaman wanda yatuna wani abu tashi yayi da sauri ya dauketa yafice da ita bayan yadauki key anan tray dasuke ijiye keys, bude bayan mota yayi yasata yashiga gaba yaja motan da mugun gudu bini bini yana tuki yana kallonta da kyar cikin ikon Allah yakai asibitin su babban private clinic ne. Yana parking yawani fito ya fanfala da gudu cikin hospital din. “Doctor help me” yayi wani ihu dayasa some few nurses da Doctors suka fito, ganin Alhaji Nura dan nanne hospital nasu yasa duk sukayi wajenshi yama kasa magana waje kawai yake nuna musu yace “my…..my” sai kawai yayi waje da sauri Doctors suka bishi daya daga cikin likitocin yana sa Nurses afito da gado suna zuwa wajen motan kaman Nura zai fashe da kuka yace “she’s not breathing namata CPR still batai responding ba” dasauri Dr yashiga saka stethoscope yace “minti nawa kenan yanzu da daina nunfashinta”? Cikin mugun damuwa Nura yace “I don’t know I just met her abayi haka, Dr please do something please, I don’t care do whatever u have to do, she can’t go like this, tanada yara biyu yan kanana, please karufamin asiri and do something” daukan Hadiza akayi aka daura agado idan kaga yanda ake gudu da ita akan gadon idan kanada hawan jini zai iya tashi Nura zai bisu cikin dakin aka hanashi aka rufo kofa, tadan karamin window kofan yake lekawa ganin ansa almakashi ana yaga rigan jikinta ana mammakala mata wasu mashina akirji gabaki daya doctors biyu da nurses hudu sun haukace ana hada defibrillator dan ayi shocking zuciyanta, hade hannu Nura yayi yakai yashafa kanshi yana juyi saikuma yasake hada hannayen duka hankalinshi atashe yace “Ya Allah karka dauki ran Hadiza yanzu please Ya Allah, nayi alkawari zanyi azumi uku kadawo min da ita, I need to tell her how much she means to me, nagayamata ina sonta haryau har gobe, and I never intend on hurting her in anyway, Hadiza is my soulmate, Maman yarana guda biyu, my life partner, Ya Allah nasan tayi kuskure da dama but please give her a second chance please give her a second chance to amend all her mistakes ya Allah ka taimakamin” wayanshi ne yashiga ringing hakan yasa ya tattaba Aljihunshi yaciro ganin Ummi ne yasa arude yadauki wayan yakai kunne cikeda tashin hankali yace “Ummi” cikeda damuwa Ummi tace “Ya jikin Anty naga ayanda kafita saisa nakira naji ko kunkai lpy, su Amal nata kuka meya sami, Mommy su bansan mezan gayamusu ba” arude Nura yace “Ummi kutaya Hadiza addu’a ki gayama su Aman suma Maman su addu’a, Ummi banson Hadiza tamutu, she means a lot to me, Maman yarana, nariga nafaro rayuwana da ita, tayaya zan cigaba da rayuwa babu ita eh Ummi?” Yanda Nura ke magana zakasan bemasan meyake fadiba cikeda so dakuma tausayin mijinta tace “in sha Allah babu abinda zai sami Anty kaji Baban Amali, Allah ubangiji yatada kafadanta, ka koma wajensu kada anemeka, kada kadamu zan kula da kowa na gida kaji Mijina” cikeda so yace “nagode Ummi ki tayani bawa Hajiya kulawa kar jininta yahau” gyadamai kai tayi tace “to Mijina zanyi, ka manta damu anan ka maida hankalinka wajen Anty tafi bukatarka, Allah yabawa Anty Lpy” ta katse wayan, komawa gaban kofan yayi daidai ana bude kofan Dr daya yafito dasauri Nura yace “doc…..” anatse Doctor yace “she’s alive!”. Wani kalan rungume Dr Nura yayi saikuma yasake shi da sauri yaxube awajen yayi sujjada yatashi sauran likitocin duk suka fito da Nurses sai godiya yake musu head Dr yace “zaka iya shiga ka dubata but kada ka tadata kafin ka sameni a office” dasauri cikeda farin ciki yace “to, to, nagode Dr” dasauri yashiga ciro wayanshi yayi dialing number Ummi dasauri ringing daya tadaga cikeda farin ciki yace “Ummi Hadiza na raye! Tafarfado” dasauri Ummi tace “Alhamdulillah Alhamdulilah!” tahau fadama su Hajiya akan wayan duk sai hamdalasuke, ahankali Nura yana jinsu yace “ina Amal da Aman”? Ita tama dauka ya katse wayan da sauri tace “Amal na kuka gatanan na goyata tayi bacci, shikuma Aman gashinan kan cinyana idanunshi biyu yayi shiru kanason kaga Mommy ka ko”? Tai maganan a tana shafakan Aman, Gyadamata kai Aman yayi ahankali, “bashi wayan” Dasauri Ummi tabama Aman wayan cikin sanyin murya yaron yace “what happen to my Mom Dady?” Murmushi sosai Nura yayi yanzu yakara tabbatar yes Allah ne yabama Hadiza second chance tunda gashi yau Aman ne ke wannan damuwan kan mamanshi yaron da is always angry with her, cikeda so da lallashi yace “Momy was a bit sick but yanzu she’s fine, tana bacci anjima zanzo gida na kwaso ku kuzo ku ganta kaji” gyadamai kai Aman yayi Nura yace “you are the only man in the house, bana nan kaine incharge so promise me you will take care of your Grandma, Aunt, Anty Ummi and little Amali, promise me zaka kula da kowa” ahankali Aman yace “I promise Dad, take care of my Mom” murmushi Nura yayi yace “to zanyi, Daddy loves you and Amali a lot ko kada kadamu anjima zanzo gida ok” “okay Dady” katse wayan Nura yayi yawuce yabude dakin ahankali ya shiga, Hadiza na kwance kan gado da kayan patient an saka mata oxygen mask a hancı har lokacin she’s still connected to some machines zuwa yayi gaban gadon ya zaune tareda kama hannunta da sauri yakai bakinshi yayi kissing yana kallonta yayi shiru, she looks so peaceful tana baccin nan babu wanda zai ganta yace fitinanniyan mata ce, sake kissing hannunta Nura yayi murya chan kasa yace “thanks for pulling through, you scare the hell out of me today Hadiza” yayi shiru yana kallonta saikuma ya rungume hannunta akirjinshi yace “I love you very very much Hadiza despite all your crazy and annoying attitude but still ina sonki that’s why I’ve been putting up with your shit all this years, ni kaina I wonder why nakeson stubborn mata irin ki, but yazanyi the love is just unconditional kada ki karamin abinda kikamin yau okay! Kin tsorata Nurin ki sosai Hadiza” yayi shiru saikuma yasake kai hannunta kan bakinshi ya manna mata kiss yana kallon fuskanta yace “bantaba tsanan kiba for once duk kalan abinda zakimini, infact sometime nakan gayama kaina ma I should be grateful inada matan da will always say what’s on her mind the way it is, babu kwana kwana that’s you Hadiza, you are so real ba kaman sauran mata ba that use to be cunny and sly, nasan halinki tsaf ciki da waje saidai na gayama mutane who u are, you are just stubborn, gaki da anger issue but u are not wicked Hadiza, and u are not evil, u don’t even have that time, baki cikin sahun matan dake bin malamai ko bokaye so sometimes I feel kome zakiyi I can put you with it because bakida mugun nufi azuciyanki kuma baki shirka and idan akwai soyayya kome zakimin zan iya hadiyewa and be the man saisa ake ganin kaman nina bataki” yayi shiru yana kallon fuskanta yace “I just want you happy, I want you to enjoy your self saisa I gave you all that u desire, Hadiza banyi aure dan to hurt you ba infact I did it for you, I did it for my children and for myself, you were not willing to change and I don’t wanna force you, danaga kin aminta da Ummi, keda baki yabon kowa but kika yabama Ummi not once, not twice yasa I looked at the girl to see menene in this girl da matane the whole Hadiza ke yaba” yadanyi shiru ahankali yace “ke kikamin auren nan Hadiza and I was still considerate to marry the girl wacce keda yaranmu kukai approving sabida karna saba miki, I don’t think akwai a man that can love his wife this much kaman ni” yayi shiru yace “I thought bana gabanki cus u don’t value me Hadiza, u don’t look at me with love and affection dakikemin kafin muyi aure, rather koda yaushe kallona kike like your mate, bantaba sanin u will react this way da auren nan ba cus banga soyayyan dakikemin ba is as if yayi disappearing, to my biggest suprise naga auren yasa kin dawo dumu dumu kinasona saisa danaga haka I always give you my attention, and my love cus I don’t wanna hurt you, I took care of you, pamper you, always showing you how much u mean to me that babu abinda ya chanza a soyayyan danake miki eh Hadiza. I want you ki tashi mu rufe wannan chapter na fada kullum, mudawo kaman yanda muke da and forget everything and live as one okay happily ever after” yayi maganan yana tashi ya manna mata kiss a goshi sannan yakara gyaramata bargo yafito yawuce office na doctor. Zama Nura yayi kan kujeran dake facing Doctor su dake duba file na Hadiza da glasses a idanu, saida yagama yadago yakalli Nura dake kallonshi yace “Alhaji what your wife had today was SCA, watto sudden cardiac arrest!” Sosai Nura ke kallonshi Dr yace “well all I can say miracle kawai yadawo da ita duba da lokacin daya daukeka da ganinta da bata CPR, dakuma kawota nan hospital still ta farfado is just God!” Ahankali Nura yace “Alhamdulillah Ya Allah, Hamdan Kaseeran Dayyiban Mubarakan fii” Dr yadan sauke ijiyan zuciya yace “zanyi managing nata a hospital for 7days dan I need to rule out daga ina wannan matsalan yafara cus this is her hospital bamu santa dawani matsalan zuciya ba nor hawan jini so inaso zan mata some test dazamu duba complete lafiyan zuciyanta tundaga kan arteries da veins da komi na zuciyan, zatayi EKG, MUGA, MRI, Exercise stress echocardiogram test, gashi u need to make payment” yabama Nura takarda ya karba dasauri yana dubawa Dr yace “Alhaji Nura” anatse Nura yace “na’am Dr” Doctor yace “so far so good we don’t know meya jawoma this issue and banso nayi digging into personal life dinku but ina ganin bayan munyi ruling out the heart issue I will refer her to a psychologist cus I think matanka is suicidal!” Dasauri Nura yace “no, no Dr, Hadiza musulma ce nasan we are having one or two issues but nasan bazata taba tunanin kashe kanta ba” Dr yace “yet kasameta abayi akasa ta kunnama kanta ruwa she knows the dangers of that, banda she’s risking jikinta ma cold that could result to pneumonia, she’s also an adult 32yrs da 2kids more of the reason why dole nayi referring nata to psychologist cus I believe batama san metakeyi ba duba da what’s at stake, what life nata means to you, to her kids and to her family” Shiru Nura yayi yakasa magana kana ganin fuskanshi kasan he’s feeling guilty he’s not just happy, ahankali Dr yace “it’s okay you have to be strong anan” gyadamai kai Nura yayi batare daya iya magana ba, Dr yace “I will suggest ka kira all family members nata, duk wani masoyanta should be here for her, koda wasa kada ku kara batamata rai for now, kutaru make her happy and show her how important she is to all of you, like I said bansan mene asalin problem din ba but I strongly believe your wife is depressed and suicidal dan haka you people should show her love” gyadamai kai Nura yayi, Dr yace “Alhaji Nura daga yanzu do kome zakayi kayi dan karta sake having this cardiac arrest dan believe me she might not be lucky the second time!” Gyadamai kai Nura yayi yace “İn sha Allah this is the first and last time” Dr yace “you can go” tashi Nura yayi yafice ahankali yafita waje wani dan dakali yasamu yazauna yayi shiru yana kallon paper expensive scans da test din zuciyan da za’amata sannan yaciro wayanshi yakira Jams ya sanar da ita komi da ake ciki yace “zai samata kudi tama kowa booking flight su taho da Mama da sisters dinta Hadiza needs love that she might be suicidal” katse wayan yayi yatura mata 1M sannan yakira Hajiya ya sanar da Hajiya ma komi, anatse Hajiya tace “Hadiza bazata taba kashe kanta ba Nura kasan likitoci da zancen banza wani zubin” Nura feeling so bad yace “Hajiya duk ni naja komiko”? Tashi Hajiya tayi daga falon ganin Ummi tafito daga kitchen tawuce dakinta ta zauna anatse tace “no Nura bakai bane kaddara ce” muryanshi na rawa yace “Hajiya I push Hadiza so hard da tana kokarin kashe kanta ko Allah yasan ban auri Ummi dan kuntata mata ba Hajiya u know me kinsan danda kika haifa am not a wicked person, inason mata ina kuma tausayinsu sabida matane kannina gabaki daya” cikeda so dakuma lallashi Hajiya tace “don’t beat yourself too hard Nura, mata munada zafin kishi, wasunmu sun iya handling kishi wasu kishin zai iya hallakasu stop blaming yourself Son, aure ba haram bane Alhamdulillah da ranta yanzu abinda zance maka is tundadai case din yakai haka karaba musu gida kaji” shiru yayi hakan yasa Hajiya tace “you have too nasan yanda kakeson yaranka su taso kansu daya but dole ka hakura dan at this point akwai cutarwa tunda Hadizan ba lafiya gwara yanzu ka dauke Ummi daga gidan nan ka kaita wani waje, idan kagama sabon gidan ka maida Hadiza chan saika ijiye Ummi anan kaji” gyadama Hajiya kai yayi yace “to” anatse Hadiza tace “kayı sallan asuba”? Sai a lokacin yaga gari yamadan soma haske ahankali yace “banyiba bari naje nayi” dasauri tace “tohhh” ta katse wayan. Karfe goma family Hadiza na asibitin dan Max air suka samu na 7:30 shima dan anyi delay, da mahaifiyar Hadiza, da Anty Jams, da kannin Hadiza guda biyu dake binta Rabi da Hafsat dukansu kowa yayi aure duk jugum kowa yayi a asibitin har lokacin Hadiza bata tashiba, Mama dake kallon Nura dake rikeda hannun Hadiza tace “kaje gida kayi wanka ka kimtsa Nura” girgiza mata kai yayi yace “bazan iyaba Mama, bari saita tashi ai Dr yace nan da awa daya alluran zai saketa ta farfado” saikuma da sauri yakalli Anty Jams yace “ga car key na jeki dauko mata su Aman idan ta tashi ta gansu zataji dadi Batai musuba Anty Jams takarba key Rabi da Hafsatu sukace zamu biki bata hanasu ba duk motan Nura suka shiga ta tada Rabi tace “wlh sainaci kutumar uban yar aikin nan dan durun uwatta” wani kallo Anty Jams tamata tana tuki tace “kinsan Allah idan abinda kike shirin yi kenan zan iya kwana naje na saukeki a asibiti” cikin fushi Hafsat tace “Anty Jams waike mesa kike abu kaman Mama, inda mu Hadiza takira da tuni bamu zo mun tayata koran shedaniyan yarinyar ba takama takiraki bayan tasan u will just talk like Mama look at her yau, inda ta mutu shikenan fa mun rasa yar uwanmu Nura yacigaba da rayuwanshi like nothing happen mukuma fa? Munrasata har abada, duk yanda zaki kalli abin Nura yariga yaci amanar Hadiza daya auri yar aikinta, ai da kishiyan gida gwara ta waje, yarinyar da Ya Hadiza tadauka aiki tamata komi I remember lokacin da Ya Hadiza muna waya tana yaban yarinyar wai tanada kirki tanason su Aman saisa take biyan yarinyar 50k ni kaina saida nayi ihu nace yar aikin kike biya 50k abinda akano 5k ko 8k ake biya duk wata, tacemin yarinyar nada kirki ne but shine munafukar ta aure mata miji akanme Ya Hadiza bazata hadiyi zuciya ta nemi mutuwa ba is it easy? anty Jams are you even relating the pain Ya Hadiza is going through everyday agidan nan tana kallon yarinyan” ta share hawayen daya zubomata da sauri tace “Wlh sabida Nuran ma babba ne kuma akwai Mama awajen da bazan gaidashi ba, munafuki kawai mayaudari mugu sai yanzu dayaga takusan zuwa barzahu shine yaşan yana sonta” Rabi tace “bar munafuki ai maza! Maza! Wlh namiji ba dan goyo bane, namiji butulu! Namiji mayaudari! Maza yan duniya! Ba kunya ba tsoron Allah ba kawaici ya auremata yar aiki!!! Wlh kaman naita surfafamai zagi dana ganshi!” Anty jams kasa cemusu komi tayi dan itama bawai she’s happy bane she’s just feeling bad ganin kanwarta in that state saida sukakai gidan tayi parking tajuyo takallesu tace “Hafsat, Rabi’a na rokeku da girman Allah kada kuyi wani abu kungamai mahaifiyar Nura na gidan bawai kuma lafiya gareta ba please” da magana ciki ciki sukace “munji” duk suka sauko suka shiga cikin gidan, Hajiya ce ke zaune a falo ga Meena agefenta dake zuba mata kunu ganinsu yasa tace “a’a su Jamila ne” Cikeda fara’a duk suka shiga gaigaisawa akayi anawa juna jaje, Anty Jams tace “ina yaran Baban su yace nazo na daukosu daganan zamu dan daukanma Hadiza kaya adaki” dasauri Hajiya tace “suna sama yanzun nan Ummi tahaura dasu dan yimusu wanka kuje kuhadama Hadiza kayan kafin nan tagama shiryasu nima ina ganin zan biku asibitin nan naje na ganota” Anty jams tace “Hajiya kina fama da kanki dakinyi zamanki agida wlh ai Alhamdulillah tunda she’s out of danger” Hajiya tace “ina kafana kafanku kuzo kuyi Kari nasan bakiyi ba” duk sukace Alhamdulillah suka wuce sama Meena tabisu da kallo zata mike Hajiya takama hannunta tace “me haka ina zaki saikace sata zasuyi agidan”? Dasauri murya chan kasa tace “wajen Ummi zani” girgiza mata kai Hajiya tayi tace “hakan zaiyi kaman munada wani manufa zuciya Jamila nada hankali ai yi zamanki anan” badan tasoba ta zauna. Daidai Ummi tafito daga bayi dauke da Amal a hannunta Aman tariga tamai yana zaune bakin gado da towel yana jiranta tafito ta shafamai mai su Rabi suka bude kofa suka shigo chak Ummi ta tsaya dantama tsorata cikinsu Anty Jams kadai tasani da duk suke kallonta, tsayawa tayi gaban bayin ahankali tace “sannunku da zuwa ina kwana” azuciye Hafsa tataho gaban Ummi tasa hannu ta karbe Amal azuciye ta nuna Ummi da yatsa tace “kina nema ki kashe mahaifiyar su shine kuma kike nan nan da yaranta bakar munafuka” dasauri Rabi tai wajen ta nuna Ummi daga sama zuwa kasa awulakance tace “ke kina gani kin auremata miji ko hmmm je asibiti kiga menene soyayya wlh na tausayi miki dudda bakijin turenci but zan miki u mean nothing to Nura, keba komi bane awajen Nura ba, Hadiza Itace komi nashi, mata ta daukeki tabaki aiki, ta biyaki da kyau, tabaki ci sha sutura but kici amananta ta hanyar aure mata miji abinda kikama Hadiza Allah yasa ama yaranki! Ama kanninki! Ama jikokinki ke duk Wanda kika hada jini dasu Allah yasa amusu!” Dan lumshe idanu Anty Jams tayi tace “Rabi and Hafsat please ku dauki yaran nan kuzo mutafi dakin Hadiza” daukan Aman Rabi tayi suka kwashi kayansu dasuka gani akan gado wanda Ummi tafito dashi suka juya harsukai kofa Rabi tajuyo takalli Ummi da kanta ke kasa tace “kuma wlh idan kina Tuna’nın kin kwace mata miji kinyi kuskure ki rubuta ki ijiye saikin dawo abin tausayi kuma yar kallo agidan nan danko Nura kije asibiti kigani nadaman aurenki yake, mema yakaishi gashi yanzu kin zama sanadin matarshi uwar yaranshi dayakeso na neman ta mutu, duk wani addu’a da bokaye da malamanki gwara ki kirasu dan amiki addu’a Allah sa kar Nura ya koraki, tana maganan suka fice wasu hawaye masu zafi Ummi taji sun zubomata dasauri ta share tafito daga dakin tawuce ta shiga dakinta ta tafi bayi dasauri ta duka tafashe da kuka sosai. Har suka gama abinda zasuyi sukabar gidan Hajiya har sawa Meena tayi taje takirata dantamata sallama zata bisu asibiti tace ma Meena taba bayan gida. Ahankali take bude idanu dasuka mata nauyi sosai, dummmm kunnenta yakeyi kaman wacce ake kwalama kira daga mesa haka takeji taji ana. “Momy, Momy, Momy wake up” rawa rawa idanunta keyi dasauri jin muryan Aman and Amali daga nesa chan na gayamata ta tashi kafin tabude idanun nata a juye tana kallon sama ganin mutanen da idanunta basa gane mata su da kyau blurr blurr take gani saichan taji murya daga nesa ance “can you see me” sake runtse idanunta dasauri tayi sannan tabude su Dr tagani akanta saikuma taji an rike mata hannu da sauri takalli hannun ganin Amali da Aman suna kallonta suna kuka har lokacin suna kiran Momy yasa azabure ta taso zaune Dr yace “woo wooo calm down kada ki tashi” dasauri tasaya dayan hannunta dake rawa zata shafa kan zaman dake kuka sosai yana shesheka Dr yatayata kama hannun tadaura kan fuskan Aman rike hannun yayi yace “Momy don’t be sick again I will never be angry with you again I promise” gyadamai kai tayi Amal tace “me too Momy” ganin yanda Hadiza ke yunkurawa tanason daukan yaran nata yasa Dr yadago gadon tayi zaman kwanciya yasada yaran yasasu ko Wanne aside nata rungumeta sukayi kuka hawaye ne suka fito daga idanun Hadiza ahankali Dr yaciremata oxygen din cikin murya mara karfi tace “A…..man, Aaa….mal” “yes Momy” kankamesu tayi kafin in a very weak voice tace “I……..na…..Da…….dy….” Dasauri duk suka dago suna mata pointing Nura dake tsaye dab da bed din yana kallonsu yana murmushi wani kalan kallon Nura tayi sai lokacin ma taganshi da duka mutanen dakin sai kawai tafashe da kuka sosai tana mikamai hannu dasauri Nura yaje rungumeshi Hadiza tayi sai a lokacin karfin kukanta yakaru ta kankame Nura sosai tanajin mugun sonshi aranta tace “Nuri kayakuri kayafemin duk abinda namak……” hannunshi yadaura kan lips nata yace “shiiiii u talk too much daga tashinki just get better I love you My Didi” hawaye na bulbulowa daga idanunta tace “I love you too my Nuri” Dr yace “tunda dai love moment ake bari naje anjima madawo atafi da ita for lab investigation, yanzu have this moment” yawuce yafita Nurse tabishi sakinta yayi Ahankali tana kallon yan dakin tace “Hajiya” dasauri Hajiya taje wajen gadon tace “naam Hadiza ya jiki”? Cikin kuka tace “Hajiya kiyakuri kinji nasan namiki laifi wlh Hajiya haushinki nadinga ji gani nayi kaman kene kika sashi yamin kishiya da yar aiki na, bake kadaiba kowama haushinshi nakeji har Anty Jams dake gayamin gaskiya da ina bayi naji numfashina yana tafiya I was trying nakira Nuri like azo ataimakamin but nakasa naji wani murya nagayamin bazakizo ba sabida na cutarda ke sannan na zargeki abisa laifin da baki aikata ba kuma baki tsaneni ba, Hajiya naji dadi da Allah yatasheni nayi alkawari dan nemi gafaranki Hajiya kiyakuri kinji” share mata fuska Hajiya tayi tace “Hadiza nobody is above mistake komi yawuce awaje bantaba rikeki ba kinji”…. *** Yau kwana uku Hadiza na asibiti tun ranan Nura bai kara kiran Ummi ba ko gida baya dawowa shike kwana da Hadiza saidai akaimai kaya, yan uwanta ne ke dawowa gida kwana su shiga kitchen suyi girki saiya zamto Ummi kullum taba daki muddin zata fito tahadu da Hafsat ko Rabi saisun yada mata habaici, takira Nura sau uku bai dagaba tamai text daban daban duk ba reply Hajiya kadai da Meena ke kula da ita dudda bata nunamusu komiba Hajiya ko ankawo abinci idan sun gama girkawa ko Ummi na sama saita kirata tazo aci abincin da ita hakanan zata sauko not feeling among, idanun Ummi sun fada babu abinda yafi damunta yanda Nura bai kirata ba ba reply kullum saitai kuka kafin tayi bacci. Yau kaman kullum wuraren 12 tana zaune ita kadai a falo Meena tashigo dakinta tace “tashi muje asibiti tare” dasauri Ummi tace “ba’ace naje ba, kinga ko Hajiya batace najeba hakama Baban Amali karnaje wani abu yasami Hadiza” Dasauri Meena tace “Hajiya takirani tace muzo tare Allah shayi akasa nahada, tashi kisa Hijabi muje bolt na kira yana waje ya iso” badan tasoba ta tashi hijab kawai taja maroon har kasa tasaka tabi Meena suka fice daman kowa na asibitin har Hajiya suka wuce. Wuraren 1:15 sukakai hospital din Ummi sai kallon asibitin take yahadu sukai ciki har zuwa gaban dakin da Hadiza ciki Meena na gaba ta window dakin Ummi ta hangi Hadiza zaune kan gado ga Aman da Amal sun rungumeta kaman zasu koma ciki Hajiya na bata kunu da spoon tanasha su Yayyinta da Mama ana hira kowa na nan nan da ita, daidai Meena tasa hannu zata bude kofan su shiga ciki kaman daga sama sukaji muryan Nura yace “Meena!” Dasauri suka juyo Ummi ta tsare Nura da idanu sabida yanda tai kewanshi yaune rana na hudu dabata ganshi ba dasauri sauri yake tahowa yana leken dakin kaman mara gaskiya yana zuwa wajen cikeda fada yanuna Ummi yana kallon Meena yace “wayace ki kawo Ummi asibitin nan eh Meena?” Wani kalan dum! Dum! Dumdum!! Ummi taji azuciyanta ta tsaya chak tana kallon Nura dake kallon Meena ranshi abace kawai yasa hannu ya karbe flask din daga hannun Meena yace “wuce kije ki komarda ita gida” daidai lokacin sukaji Hadiza tace “Hajiya kaman muryan Nuri na nakeji ko” dasauri yayi kofan yace “gani nan My Didi” yashiga ciki ba Ummi kadaiba har Meena jitayi ranta ya sosu da abinda Nura yayi daurewa Ummi tayi iya daurewa takalli Meena cikeda Fara’a tace “kingani saisa nace miki bai dace nazo ba Hadiza batada lafiya, baidace ta ganni ba kiramin bolt nabishi nakoma gida kesaiki zauna” Meena batace komiba cikeda bacin rai tashiga tafiya tana neman bolt Ummi dan juyawa tayi takalli cikin dakin Nura na kusada Hadiza ta daura kanta a kirjinshi yana shafa mata kalaban kanta da wani kalan shaukin so dayan hannunshi yana nuna mata hotunan bikinsu sai murmushi suke both ita da shi looks so happy, hawaye Ummi taji sun zubomata da sauri tasa hannu ta goge tajuya dasauri tawuce awaje tasami Meena daidai bolt yazo Meena zata shiga Ummi takama hannunta tace “Meena dan Allah sabida ni kada ki fasa zuwa wajen Hadiza ki gaidata please kije nizan koma gida ni kadai please dan Allah” Meena da idanunta sunyi jaaa tace “Ummi sakeni” cikin lallashi Ummi tace “inhar kinasona da gaske ki koma nizam koma gida please Autan Hajiya” badan tasoba takoma Ummi tashiga motan bolt yaja motan suna fita daga asibitin Ummi tarushe da kuka sosai dasauri mai bolt yajuyo yace “Hajiya lafiya”? Cikin kuka muryanta bama yafita da kyau tace “bakomi kawai mutafi” yanda take kuka harda shesheka saitaji ta raina kanta duba da yanda Hadiza keda komi, she’s surrounded da family dake sonta ga Miji ga yara saitaji ta raina kanta, batada kowa batada komi! Allahu Akbar! Ranta ya sosu yau takara tuna ita marainiyace Mamanta ta rasu! Babanta yarasu! Kakansu kadai gareta data tsufa tukuf sai kannenta yara su Shatu su biyu 12 and 13yrs, jibi yanda Nura yayi da ita yau kaman wulakantacciya mara daraja! Yasa she felt like she’s nothing to him! Yasa taji she don’t belong anan a family nan, ahankali ta bude yar jakan data dauka taga tanada kusan 15k aciki cikin muryan kuka tace “direba dan Allah kaini tasha dazan sami motan Adamawa yola” Dasauri direba yace “location zamu chanza kenan jabi garage za’a samu” cikin muryan kuka tace “kaini” nan yakaita har inda ake lodin Adamawa Yola tabiya direban 2k tana zuwa tabiya 13k kudin mota amman sai dare motan zai tashi tafiyan dare ne tanemi waje kawai ta zauna takifa kanta kuka take mai tsuma rai bana wasaba, gani take ko Mudi baitaba hurting nata this way ba dan shi physical damage yamata na duka dasauransu, Nura just crushed her fragile zuciya dake cike da dumbin sonshi azuciyanta kafin yakoreta gabadaya agaban jama’a gwara takoma kauyensu ya biyota da saki takara rushewa da kuka. Wayyo Allah na Ummi😭 Kai Maza maza maza!! One word for men please cus suna bani ciwon kai. What exactly keep a Man?? Sex? Happiness? Respect? Ko Loyalty??? The list is long but in your opinion what keep a Man? 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣0️⃣ @TRENDYOUTNET Modest fashion world ne inda zaki samu professional kayan zuwa office masu kayatarwa, kyawawa, masu suturta jiki da mutuntawa, idanma casual kaya kike nema na sakawa yau da gobe duka tanada sunadashi all you have to do is chat them up ta wannan number wa.me/+2349093300112 Kokuma zaki iya zuwa shagonsu dake nan Shop C22C 2nd floor Platinum Mega Mall opposite Ultra Modern Market Behind Next Cash and Carry Jahi, Katampe Road Abuja And u can also check shagonsu a IG @trendyoutnet don’t forget to follow them🔥 cus anayi baki😅 20 Saida tayi kuka ta koshi sannan tadago kanta taciro wayanta daga jaka tareda mikewa tabar wajen taje chan wajen wata bishi ya ta duka awajen, duk duniyan nan batada kowa banda kakanta duk wani abu data iya yau aduniya kakarta ta koyamata, Kakarta is her everything. Dialing number ta tayi yana ringing ta daga tace “Yar Albarka kinganni nan fa tundazu nake jinki araina amman Shatu nake jira tadawo tazo ta tayani kiranki amman ina tanachan tana buga yar gala gala, ya kike yar Albarka ya mijin naki da kowa da kowa”? Kungane feeling dinnan da yaro yakeji idan yana cikin damuwa yaji muryan iyayenshi kawai sai Ummi ta rushe ma Gwaggo da kuka, hankali tashe Gwaggo tace “ke! Meya faru kike kuka haka? Waya tabamin jikata iyye? Rabonda naga kinyi kuka haka tun zamanin azzalumin nan Mudi, meya faru kike kuka Ummi? Ya isa, ya isa, bagani ba, da raina fa Ummi kike kuka haka sokike Mamanki tayi fushi dani bayan tabani amanan ku, dena kuka kinji komeme ina nan fa, da raina kuma oya ya isa, zan iya saida raina naga bakuda matsala arayuwan nan, ishuru Zainabu ishiru kinji, wayataba mini yarinyata mai hakuri da kawaici da kunya? Wayatabamin jikana?” Cikin wani kalan kuka Ummi tana shesheka tace “Nura!” Salati Gwaggo tayi da sallallami tace “Nuran ne yasamin ke kuka haka? Mutumin danaganshi tsofai tsofai dashi zai iya haifanki sau biyar shine zai sakamin jika kuka haka? Shi baisan badan naganashi tsoho babban mutum mai hankali daban yarda nabashi ke ya aure ba, wato yagama tsotse kuruciyanki zai fara miki tijara, meya miki? Share hawayenki fadamin meya faru, fadamin daga tushe zuwa reshe share hawayen ki imaza, inajinki” share fuskanta Ummi tayi kaman yar baby tana kuka ahaka dai tabama Gwaggo labarin komi dake faruwa gabaki daya bata boyemata komiba har zancen kannin Hadiza, Gwaggo tace “amman mijinki yabani kunya Ummi, sabida shi tijararre ne katon banza, da girmanshi da tsufanshi bai amfaneshi ni zaizo har gidana ya auremini ke, wato auren huce takaici yayi, yazo ya chusama jikana soyayyan shi a zuciya haka sannan ya wulakanta mini diya? Jibi yanda jikana ke kuka a tasha gaban dubbannin mutane sabida shashashan Nura” Gwaggo tayi shiru tana karajin yanda Ummi ke kuka ko ba’a fada mata ba taji tsananin soyayyan Nura atattare da Ummi, wannan karan ne yatta tafada soyayya bata taba son wani ba Ummi, lokacin da akamata auren Mudi bamatasan menenen soyayya ba, da ace Ummi batason Nuran datace mata tadawo gida dan dudda tana yar kauye tasan darajan jikokinta, lokacin da Mudi ke kirbama Ummi duka tasan taje ta dauko jikanta tadawo da ita gida, tayi shige da fice akauyen nan maigari da manyan gari tasa aka raba auren, dudda Mudi nashigowa har gida yadakesu still batasa Ummi takomamai ba saidai tasan yanda tayi tafitar da Ummi daga kauyen, ina bata yarda awulakanta jikokinta ba. Ijiyan zuciya tasauke ahankali tace “Zainabu” ahankali Ummi tace “na’am Gwaggo” Gwaggo tace “Ummi dudda mu yan kauye ne ba yan binni ba Ummi nabaki tarbiya nakoya miki dabarun zaman duniya ke Ummi ko birnin sin aka kaiki zaki iya zama cikin mutanen yan boko sannan ki samama kanki lafiyayyen waje dan haka share fuskanka, Alhamdulillah ina raye ban mutu ba, Nura ne dai ko wlh sai yasan yayi rashi dan jikata daban take acikin jikoki dubun dabara!” Gwaggo tace “dudda za’ace kinyi gajen hakuri dakika taho ai aure ya gaji yau ayi fada yau ashirya but ni kakarki nayi na’am da tahowan ki Ummi idan Mata da Miji natare inhar akwai soyayya to ka tsaya koma wace ukubace zaka iya jajircewa ka maganceta amman in babu soyayya a auren gwara kayi gaba, abinda Nura yamiki ya nuna kaman dama chan baitaba sonki ba yakawai aureki sabida ya farkan da sumammiyan matanshi Hadiza ne yanzu kuma data farka baida bukatanki dan haka saurareni nan Ummi kibawa Nura tazara harsaiyasan amfanin ki, ke koda baya sonki ke wlh ma yayi karya yace baya sonki, Ummi nabaki tarbiya da dabarun zaman duniya duk wanda yazauna dake saiyaji yana sonki Nura na sonki kawai bairiga yasan dahaka bane amman yanzu zai sani, kalleni nan bazaki dawo adamawan nan ba, sabida zai biyoki nan barni dashi yazo nemanki wlh wlh daina mishi wankin bargo zan solleshi tas, saizan yarana nada daraja kuma babu abinda bazan iyaba akanku ku ukun nan, kinsan mezakiyi yanzu?” Dasauri Ummi tace “a’a” tace “kowa yariga yasan ke yarinyace mai tarbiya da hankali ce baikamata kitashi farat daya kibar gidanba yakamata ki sanar da wani babba yanzu Hajiya na asibiti kada ki kirata dubama da bawani lafiya gareta ba kira kanwar Nura dakika gayamin kwana kin baya kunyi waya wacce bata kasan kiraya maza maza ki gayamata cikin hikima kinji” Gyadamata kai Ummi tayi Gwaggo tace “koyaya kukayi ki kirani kisake sanar dani wayata na hannuna”. @TRENDYOUTNET Modest fashion world ne inda zaki samu professional kayan zuwa office masu kayatarwa, kyawawa, masu suturta jiki da mutuntawa, idanma casual kaya kike nema na sakawa yau da gobe duka tanada sunadashi all you have to do is chat them up ta wannan number wa.me/+2349093300112 Kokuma zaki iya zuwa shagonsu dake nan Shop C22C 2nd floor Platinum Mega Mall opposite Ultra Modern Market Behind Next Cash and Carry Jahi, Katampe Road Abuja And u can also check shagonsu a IG @trendyoutnet don’t forget to follow them🔥 cus anayi baki😅 Kiran Ya Aisha tayi ringing daya Ya Aisha ta katse wayan takira Unmi back kafinma Ummi tayi magana tace “Ummi ai dama ina shirin kiranki yau nace kwana biyu bamu gaisa ba, to ya kike” cikin muryan Ummi da baya fita sosai tace “lafiya l…..” “Ummi, meya sameki kikai kuka haka har muryanki ya chanza”? Ya Aisha tai tambayan da sauri Ummi tarasa mesa aka tambayeta sai tahau kuka da kyar tace “Ya Aisha kiyakuri kada kiyi fushi dani saisa nakiraki inaso ki lallashi Hajiya itama kada suyi fushi dani amman zan tafi kauyenmu wajen Gwaggona gani nan atasha” dasauri Ya Aisha tace “mene! Ummi! Mesa zaki tafi? Meya faru? Fadamin kinsa gabana nafaduwa menene”? Ahankali Ummi ta rairamata komi daga AzuwaZ Ya Aisha zuciyanta yafara tafarfasa sosai tace “sabida yar gwal dinshi zai wulakanta ki? Ai wlh Ya Nura kaman na dakeshi wani zubin bantaba ganin kalan mutum mai zuciyanshi ba Mata tazagi mahaifiyar ka ka kasa komi haba” tayi shiru tana sauraron yanda Ummi ke kuka tace “Ummi kema saiki tashi kitafi mesa baki fadama Hajiya ba? Hajiya bazata taba bari Nura ya wulakanta kiba wlh yayi kadan yayi irin abin nan agabanta ai shi yasan waye Hajiya idan tai fushi ko duka kano zasu hadi ba’a iya lallaso ta kuma wlh bazakije Adamawa ba zai gane yamiki laifi yaje har garinku ya auroki marainiya dake shine yanzu zai fara wulakantaki wa zaki kalla kiji dadi? Zaman wa kike? Yan uwan Hadiza sumiki kinyi shiru sunzo gıda sun gaje kitchen though nagane dalilin dayasa Hajiya bata musu magana ba amman dudda haka gwara dakika barmai gidanshi dan suka dawo ma wulakancin saiyafi nada….” Ya Aisha tahau surfafa masifa kafin chan tace “Ummi kiyakuri kinji amman dan Allah kada ki rabu da Yayana but na yarda yanzu kada ki koma gidan kiyi fushi dashi amman dai kada kirabu dashi wlh zai koma gidan jiya kin tsamoshi daga kangin dayake ciki kin maidashi mutum kin rufamai asiri kuma ke Ummi kinma Ya Nura komi fan Allah kada kiyi fushi dashi yanzu kinsan mezamuyi zan kira wani kanın Mijina yazı ya daukeki ya kaiki gida zanyi arranging komi amiki international passport da visa da sauransu Mijina duk yanada hanyan da za’amiki fast saikizo wajena Ummi zan gyaraki wlh sai Nura yamiki kuka kafin ki koma wajenshi kinji dan Allah Ummi kada ki koma garinku” Ahankali Ummi tace “Gwaggo na bazata yardaba nariga nagaya mata zan dawo gida” dasauri Ya Aisha tace “kira Gwaggo hadamu conference call kin iya hada conference call”? Ahankali Ummi tace “a’a” Dasauri Ya Aisha tace “turamin number ta” tura mata number Gwaggo tayi sunyi waya mai tsaye sannan Aisha tasake kiranta tace “Gwaggo tace takirata” kiran Gwaggo Ummi tayi tana dauka Gwaggo tace “kije wajen kanwar nan nashi Alhamdulillah yan Yan uwan shi duka suna sonki, kidena kuka zamuyi magana idan kinkai gidan kanin mijinta ki kashe wayanki but kullum kidinga kunnawa kina kırana sau daya muna magana inji lafiyanki kuma nagayamata kada tafada ma kowa kina wajenta tace haba bazata fadi ba, bari Nura yadawo daidai zai gane yayi rashi, jikata daya ce tak acikin mata miliyan” katse wayan tayi Ya Aisha takira tace “me Gwaggo tace”? Ahankali Ummi tace “tace naje wajenki” murmushi Ya Aisha tayi tace “Alhamdulillah Alhamdulilah kina tashan jabi ko” Gyadamata kai Ummi tayi tace “um” nan da nan ta katse wayan kafin chan tasake kiranta tace “gashinan zuwa nabashi number ki kada ki kara kuka Ummi, kinga maza wlh halin maza saisu saisa wasu ke cewa gwara kaci ubansu dan sunfison matan dake basu wahala suke basu kashi ada ban yarda da maganan ba but wlh yanzu akan yayana uwa daya uba daya na yarda, idanma tunani yake baki da gata wlh baiyi tunanin da kyau ba Ummi nadade banga Kakan dakeson jikokinta kaman Gwaggon ki ba ko ita kadai ta ishi ya Nura ai zaije kauye nemanki wlh saitaci mishi mutunci, butulu kawai gwara da kika bar musu gidan indai Hadiza ne gashi ga ita ai hali zanen dutse mai hali baya fasa halinsa ayi soyayya agama yanzu idanunshi zasu budene ya nemeki”. Sosai Ya Aisha take mata hira awaya just to ensure bata kara kuka ba har Faisal yazo ganin call waiting na shigowa wayanta yasa Ummi tace “wani number nakirana Ya Aisha” dasauri Ya Aisha tace “shine dauka” katse wayanta tayi tadauka suka gaisa yace “ina gaban yola line kina ina”? Tashi tayi ta taho wajen harta ganshi suka gaisa yabude mata baya tashiga tazauna yabata ruwan gora mai sanyi ta karba tamai godiya suka tafi gidansu mai kyau babba ne matanshi dakeda tsohon ciki tama Ummi sannu da zuwa suka kaita daki lafiyayye matan tazauna da Ummi sannan tafita takawoma Ummi abinci da drinks da kayan sawa da yawa tasamata a sip Ummi tamata godiya. 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPİSODE 2️⃣1️⃣ Ina mata masu sha'awar koyon sana'ar saƙar kwarashi ta zamani? Ko kina da labarin Heart Stitches kuwa? Zata fara online classes na koyarda sakar kwarashi nan bada jimawa ba. Ita wannan saƙar idan kin iya ta, kina zaune gidanki zaki dinga yi kina saida abun da kika saƙa cikin sauki. Gashi kuma tana saida haɗaɗɗun handmade bags. Ki shiga group ɗinta domin ƙarin bayani ga link din 👇🏼 https://tinyurl.com/bagsstitcheshaven Kiyi following page dinta kisha kallo. https://www.instagram.com/heart_stitches77 Zakuma ku iya chatting nata up ta hanyar danna this link; https://wa.me/2347034845999 21 Wajajen magrib suka shigo gidan as usual Meena direct dakinsu tawuce dan ranta amugun bace yake tun dazu darana duk wanda ya tambayeta meke damunta tace ciwon mara take, binta da kallo Hajiya tayi ta kwalama Ummi kira ganin bata afalo. “Ummi Ummi” tabe baki su Rabi sukayi suka wuce ciki Hajiya tace “hala salla take nima bari naje nai salla” mahaifiyar Hadiza tace “ina gani kam dan da yanzu tazo tamana sannu da zuwa” wucewa daki Hajiya tayi ganin Meena kan gado yasa tace “Waike lafiyanki kalau kiketa kumbure kumbure ke kadai” tana kwance kan gadon tace “cikina ke ciwo Hajiya” kanta Hajiya ta shafa tace “sannu to kinji Auta na” dan murmushi kadan Meena ta mata Hajiya tawuce tazaga bayan gida tayo alwala tayi salla tana zaune kan dadduma wanda dama haka take har akai ishai tayi tai yan addu’o’inta tashafa saikuma cikeda damuwa tace “Meena kinga je sama dan Allah ki dubomin Ummi bantaba shigowa gidan nan nakai war haka yarinyar nan batazo wajena ba, kinji muryan su Aman fa suma sai kwalamata kira suke, tashi dan Allah dubomin ita Allah sa lafiyanta kalau ba zazzabi bane ke damunta dan abinda zai hana Ummi saukowa gaisheni babban abune” daidai lokacin Anty Jams tabude kofan tace “Hajiya angama abinci kufito muci” anatse Hajiya tace “to bari Meena takiramini Ummi Jamila ganinan zuwa” tashi Meena tayi tawuce sama itama Hajiya tafito falon tasami waje ta zauna. Dakin Ummi tashiga Meena tabi dakin da kallo yanda suka barajı dazu haka yake dasauri tace “Ummi” shirun yayi yawa hakan yasa tawuce wajen bayi tabude bayin but Ummi bata ciki dasauri tafito tashiga bude dakunan yaran ganin Aman adakinshi yasa tace “Aman have you seen Ummi”? Cikeda rashin jin dadi yace “no Aunt I can’t find Anty Ummi anywhere” dasauri dasauri Meena tafito tasauka kasa Hajiya data bita da kallo ganinta ita kadai tace “ina Ummi”? Dasauri tace “ina zuwa Hajiya” saita wuce kitchen tabude kofa taje backyard batanan dasauri tawuce wajen gateman dinsu tace “Yallabai dazu damuka fita Ummi ta dawo”? Dasauri yace “bata dawo ba babu wanda yazo gidan banda ku dakika dawo yanzu” Dasauri Meena tabude bolt na wayanta zuwa history nan taga Jabi akakai Ummi that means she changed the trip dudda haka takasa gasgatawa, part of zuciyanta nacemata Kodai bolt direban ya saceta ne nan da nan takira Number bolt driver yana dauka tamai explaining tace “ina sister na data biyoka”? Dasauri yace “Madam she was crying seriously in the car and asked me to take her to jabi garage Adamawa line” dasauri Meena hannunta da jikinta har rawa suke taciro number Ummi takira but wayanta akashe da gudu takoma cikin gidan Hajiya data kasa zaune takasa tsaye dan hakanan zuciyanta ke gayamata ba lafiya ganin Meena yasa tace “ina Ummi?” Sai kawai tafashe ma Hajiya da kuka tace “Hajiya wlh duk laifina ne” yanda gaban Hajiya ke faduwa batasan sanda tama Meena tsawa ba. “What happened what did you do Meena?” Kallon yan uwan Hadiza dake falon Meena tayi saikuma tace “Hajiya muje daki nagayamiki” ran Hajiya abace batajin zama ta iya moving kafafunta ba tace “tell me anan Meena, idan kin boye musu bazaki boyema Allah ba” Dan lumshe idanu Meena tayi tace “Hajiya naga how sad Ummi was akunshe adaki shine dazu da kuka kirani nakawo shayi naje na sameta tazo muje asibiti taki tace ba’ace tajeba shine nace kene kikace nazo da ita shine tabini………” tabama Hajiya daga farkon labarin har karshe zuwa wajen bolt Hajiya kawai ta daurama Meena mari! Saida kowa yazabura Maman Hadiza tace “assha, assha Hajiya dan Allah kiyakuri” Rabi da Hafsat zuciyanshi kaman an watsa ruwan sanyi sabida dadi, ran Hajiya yanaci bana wasaba kallon Anty Jamila tayi cikin kakkausan murya tace “tashi kitafi asibiti yanzu yanzun nan Jamila, kekuma kiramin Nura da wayanki” tama Meena dake share fuska magana azafaffe Maman Hadiza tace “Hajiya calm down bakida lafiya fushi haka baida kyau agareki” cikin tsananin fushi tace “I don’t care! Koda zan fadi na mutu awajen nan I don’t care! Kiramin shi nace!” Hajiya tafadi ranta abace kowa yaja bakinshi yayi gum babu wanda baisan labarin Hajiya ba batada kyau tai fushi Anty Jams ta tashi sun sun taje ta dauki key motan Hadiza tafice, ringing daya biyu Nura yadaga strictly Hajiya tace “kome kakeyi Nura a asibitin nan kabarshi kazo gida yanzun nan ga Jamila naturo asibiti tazo ta zauna da Hadiza” zaiyi magana Hajiya ta katse wayan takalli Meena tace “bacemin daga gani, kuma ku tashi ku kwashi abincin nan ku wuce kuje chan sama kuci” Hajiya tama su Hafsat tsawa duk suka tashi Falon yarage daga Mama sai Hajiya tazo gefen Hajiya tariketa cikin kwantar da murya tace “Nura bai kyauta ba dudda kuwa Hadiza diyata ce amman kiyakuri baya hayyacinshi kinsan ba kowa ne ya iya handling pressure ba, dan Allah kiyakuri Hajiya fushi nan baida kyau agareki” lumshe idanu Hajiya tayi sai kawai ta zauna Mama tazauna kusada ita tadauki ruwa ta bata Hajiya ta karba tasha. Cikin 20min Nura yashigo gidan adan tsorace dan yadauka ciwon Hajiya ne yatashi yana shigowa falon suka hada ido wani kallo data mai saida gabanshi yafadi wlh dasauri Nura yazo wajenta yaduka yana kallonta yace “Hajiya menene? Wani abu yafaru ne? Jikinki ne? Mama meya sami Hajiya”? Yayi maganan cikeda so dakuma kulawa ga Mamanshi nuna kanta Hajiya tayi tace “Nura tunda kai aure yau shekara goma zuwa gomasha kenan nataba saka a hanya mara kyau?” Dasauri ya girgiza kai yace “a’a” tace “nataba cemaka ka bakanta ma Hadiza koka kuntata mata, kai nama taba gayamaka ga yanda zaka tafiyar da gidanka?” Dasauri yace “a’a Hajiya, Hajiya meya faru waya bata miki rai haka eh Mamana”? Bubbuga kirjinta Hajiya tayi tace “Nura ni uwa ce, na haifi mace na haifi namiji, nasan darajan yara, banda haka d’a nakowa ne, abinda bazanso ama nawa ba wlh bazan taba bari ama nawani ba” Mama tace “kwarai!” Hajiya tace “Nura Ummi ta daukeni matsayin uwar da batada shi, bamata min kallon maman mijinta sai mahaifiyarta, bata kyashi tashiga kitchen tadafamin abincin dazanci takuma dafa na gida, wlh wlh abinda Ummi kemini ko Meena diyar dana haifa da cikina batamin, tabani abinci, ta kwashe kayana takai washing machine ta wanke tazo ta goge, ta gyaramin wajen kwana ta kunna turare, idanba na kora Ummi ba ko nace tabarwa Meena wannan tayiba yarinyar nan ita kemin komi da murmushi kan fuskanta Nura yau karasa wanda zaka wulakanta sai Ummi?” Cikeda mamaki yake kallon Hajiya danshi ya manta yama Ummi wani abu dasauri yace “Hajiya mena mata kuma? Takikkirani tun shekaran jiya ban samu nakirata back ba ban mata reply message ba shinefa kuma ai ban natsu bane” sosai Hajiya ke kallon Nura jin yau kwana uku rabon dayamayi magana da yarinyar tanason tai magana Mama tace “Nura bakai magana da Matarka ba yau kwana uku tana matarka koma menene ai ka kirata kaji ta tashi lafiya tunda hakki ce agareka gaskiy……….” Hannu Hajiya tadagama Mama azuciye hakan yasa Mama tai shiru ganin yauwa ran Hajiya alalace yake, Hajiya na kallon Nura dake gabanta aduke tamike tace “Nura auren huce takaici ko auren sha’awa fadamin wanne kayi da Ummi?” Nura na kallon Hajiya yama kasa magana saikuma yace “kaman ya Hajiya”? Cikin fushi Hajiya tace “how dare you Nura baka kira yarinyar nan for 3days kaji yatake ba you think is okay, dazu Meena takawota asibiti da sunana kamata koran kare!” Mikewa tsaye dasauri Nura yayi yashafa kanshi zuwa fuska yakalli Hajiya yace “Hajiya wani irin koran kare? Cewa Meena nayi tawuce takomar da ita gida is not good Hadiza dake that condition taganta” cikin fushi Hajiya itama tace “wat do you mean by that Nura are you trying to say Ummi tasa Hadiza in that situation”? Cikida gajiya da maganan yace “Hajiya no bahaka nake nufiba amman dai ai aurenta danayi yasa Hadiza ke neman rasa ranta so I have to keep her away from Hadiza kada tazo takara samin heart attack, am just protecting Hadiza Hajiya” Sosai Hajiya kewani kalan kallon Nura the way he said everything da zuciya daya kai tsaye is as if Nura baida single feeling for Ummi aranshi all abinda ke ranshi ke kuma damunshi ayanzu is just Hadiza he sees nothing wrong a abinda yayi, jinjina kai Hajiya tayi irin na manya cikin wata kalan murya tace “ai shikenan Nura tunda aurenta shine dalilin dayasa Hadiza ke neman rasa ranta saisa ka wulakantata baka daukan wayanta, tazo asibiti kuma kamata kiran wulakanci dacin mutunci Ummi ta tafi garinsu! Tabarmaka gidanka!” Dawani kalan sauri yakalli Hajiya sake jinjina matakai Hajiya tayi yanzu damuka dawo mun nemata sama da kasa bata, Meena ta duba bolt taga ta chanza location ta tafi jabi takira mai bolt wai yakaita Adamawa line” kusan shiru falon yayi na kusan minti biyu duka abinda yafaru dazu a asibiti na dawowa Nura jiyayi ranshi yabacı matuka, cikeda bacin rai yace “yanzu sabida dan maganan danayi wanda da Meena ma nayi magana bada itaba shine ita mai zuciya tawuce ta tafi garinsu”? Sosai Hajiya ke kallonshi cikin tsantsan bacin rai yace “ai shikenan Allah kiyaye, nina tafi asibiti” yajuya fuuu zai fita haryakai kofa Hajiya takirashi tace “Nura!” Juyowa yayi idanunshi sunyi jazur yakalli Hajiya tace “Nura kasani abin nan dakayi nikamawa” cikin fushi sosai Nura yace “Hajiya wai mekike cewa haka? Idanma ita nama fadan menene ba matata bace? Bazan iya ma matata fada ba? Niba mijinta bane? Itane sarkin zuciya takama ta tafi bazata iya fahimtan wat am trying to do ba, inbar Hadiza tamutu sabida Ummi? Inbar Ummi tashiga dakin sabida banso nabata mata rai eh? Things are not done like that Hajiya? Taje bazan kirata ba bazan bitaba idan tagaji da zama tasan hanya tadawo Abuja inba hakaba tayi zamant……” Tass! Hajiya ta daura mai mari abinda bata tabayiba, yadafe kubcinshi yana kallon Hajiya, dakuwa Hajiya tamai tace “kaci mai garinku Nura kaji u are very stupid, how dare you call yarinyar dake kula da mamanka all this sort of names Nura kasan bakason yarinyar nan why did you marry her? Ubanme yakaika ka aureta eh? Naga ba ita tace tana sonka ba, kotace lallai saika aureta kaika nemeta, kaiharka isa kayi magana haka akan Ummi data taimakeka da gidanka da yaranka dani uwarka, kazaci zaman ka nake agidan nan shashasha dakai zaman Ummi nake wlh agidan ma right from day one danazo itane komiba, yarinyar dake kula maka da gida da yara, tarbiyan su waye ajikin Aman da Amal Ummi, how dare u say such things about my precious daughter ina tarbiya ka da hankalin yaje eh, Nima da izinin Allah gobe zan barmaka gidan kome kaga dama kayi kuma kasani ba Ummi ka wulakanta ba ni mahaifiyar ka ka wulakanta dan yarinyar nan tadaukeni amatsayin mahaifiya, the poor thing tariga taga baka sonta baka bukatanta gwara ta koma garinsu kafin kamata kora da hali, kaji kunya Nura girmanka bai amfaneka da komiba indai wannan ne kalan rayuwan daka daukama kanka mayaudari kawai, innocent yarinya marainiyan Allah kawulakanta haka sabida burinka yacika yanzu shikenan kaje kada ka nemeta bazance kayi ba Ummi ko’ina kike Allah tsare ai Meena nada number kakarta zan kira naji kaje kayı duk abinda kakeso just know this wlh gobe zan bar gidanka kaji na rantse maka” tajuya fuuuu zata wuce dasauri Nura yataho gabanta yasha yayi kneeling tareda rike kafanta yace “Hajiya dan Allah ki yakuri baki fahimceni bane, dan Allah kada kiyi fushi dani Hajiya dan Allah dan Allah Hajiya kiyakuri” hankade kafanshi Hajiya tayi tawuce dakinta tarufe kofa tana kallon Meena dake kuka. Ahankali Mama tace “Nura baka kyautaba a gaskiya bahaka ake zama da mata biyu ba, nasan Hadiza batada lafiya kuma i get you are doing everything possible kaga tasami lafiya kar hakan yasa ka tauye hakkın Ummi wacce itama matace agareka, hakkine akanka kaje ka ga lafiyanta akullum ranan duniya which bakayiba, ita dutse ce kwana uku bata daura ka a idoba, batai magana dakaiba tazo asibiti ai ka kaita gefe kamata magana mai dadi ba kamata koran wulakanci ba kodako da Meena kake magana ai agabanta ne, kazaci bazataji ba dadi bace mahaifiyar ka na maka fada kuma kana kiranta sarkin zuciya, Allah kiyaye, tagaji da zama zata dawo, haba Nura fisabillahi fa? Haka ake magana? Kanada kanni kuma Kanada diya mace kaima Nura haba” shafa kanshi yayi yayi huci mezafi yace “Mama gida nawa akeso naraba kaina tsakani ga Allah eh? Ga Hadiza ga Ummi yanzu kuma Hajiya eh Mama”? Cikeda tausayi tace “yanzu tunda Jamila na wajen Hadiza, jekabi sahun Ummi kaga, ka kuma gwara kiranta awaya ko Allah zaisa kasameta ni zanji da mahaifiyar ka”. Wucewa yayi kawai yajuya yafita su Rabi dake sama wani tsalle sukai suka rungume juna zokaji dadi kaman zasu zare. Mota Nura yabude yashiga yaja motan yayi nisa yana tuki sannan ya gangara yayi parking tareda punching car steering da hannu yana wani huci gabaki daya ranshi ya dagule ranshi abace yake sosai bana wasaba, hannu yasa a aljihu yaciro wayanshi yayi dialing number wayan Ummi yakai kunne wayan akashe cire wayan yayi daga kunne ya jefar yasake punching car steering kaman shine yamai laifi yace “damn it” ya fuzar da iska chan yace “ni zaki gwadama zuciya? What? Can’t you just be a little Patient dani Ummi sabida kin kirani ban amsaba, what me kikeso? So kuke ku kasheni? Ku rabani biyu kowa yadauki part daya nabar Hadiza ta mutu sabida ke? Ke mai zuciya kin kama kin tafi kina kashe waya ai sai kije Allah kiyaye I will not look for you nor follow you” yayi maganan ranshi a bala’in bace kaman ba Nura ba abun yamai mugun ciwo, tada motan yayi yajuya yayi nisa sai kuma yakara daukan kwana yatafi jabi har Adamawa line yafito kawai ya tsaya yana kallon wajen that looks empty motoci duk sun tafi tsaki yayi yace “kin kyauta” yakoma cikin mota yatada motan yatafi gida yakoma yayi parking ya tsani arayuwanshi Hajiya na fushi dashi parking yayi yafito yashiga gidan direct dakin Hajiya yawuce kofan yabude Meena yagani tana bacci Hajiya kuma zaune tayi shiru kana ganinta kaga damuwa akan fuskanta ga wayanta a hannunta kallo daya tama Nura tadauke kai ahankali zuwa yayi yazauna ahankali agabanta yakama hannunta murya Chan kasa yace “Hajiyah” kallonshi Hajiya tayi duk yanda tadaure saiga hawaye tace “Nura I know baka batamin rai kasafai amman yau ka matukar batamin rai, Nura nasan kanka yayi zafi but no matter what you are going through bai kamata kama yarinyar nan ihu kamata koran kare batare daka tsaya kun gaisa ba bayan bata ganka ba ko saka a ido ba na kwana uku haba Nura yarinya mai hankali haka, ranan da abin nan yafaru agabana naji tace ka manta damu anan ka kula da Hadiza ita zata kula damu, Ummi musulma ce kowa yaje yaduba Hadiza banda ita bamu gayamata komiba batasan me akace game da Hadiza ba atleast daka ganka the least you could have done was ka kirata gefe kamata bayani gashi gashi ka rakasu su tafi amman kamata haka haka akeyi? Ka nuna baka damu da ita ba, Ummi ba zamana takeba zamanka take kaine mijinta she must have felt baka bukatanta yanzu baka sonta saisa kamata haka ta tafi tabaka sararin dakakeso are you happy yanzu kalli wayana” tanunama Nura wayan hannunta tace “nakira number yafi sau goma baya shiga na kakanta ma haka idan wani abu yaje yasami yarinyar nan ahanya fa Adamawa ba kano ba chan gari da nisa eh, Nura baka kyautaba koma menene kaci mutuncin Ummi, ka masifan bakantamin rai Nura” Hajiya tashiga matsan hawaye cikeda bakinciki Nura was just feeling bad badan Ummi danshi baiga abinda yamata ba but sabida kukan da mahaifiyarshi keyi, hannunshi yadaura kan fuskanta yana share hawayen yace “Hajiya dan Allah kiyakuri nayi kuskure bazan karaba kuma İn sha Allah zatakai gida lpy bari ana sallamalı Hadiza ta dawo gida zanje na daukota dakaina kinji Hajiya” gyadamai kai tayi tace “amman nidai gobe zanbar gidan nan kamana booking jirgi” dasauri Nura yace “appointment dinki next week fa” cikin kuka Hajiya tace “wlh nahakura da appointment, ina bukatan fresh air, Nura banson rayuwan dakakeyi da kasan bazaka iya adalci ba dabaka auro Ummi ba in the first place, bace wa nake son dakakema Hadiza kuskure bane a’a shi soyayya Allah ke daurawa mutum amman Nura ka kyautatama mai kyautata maka, ka farantama mai farantamaka, Nura Ummi has been there for you for yaranka thanks to that girl gidannan is running smooth amman bakomi kayi duk yanda kaga dama” kusan har asuba da Nura da Hajiya na zaune lallashin Hajiya yake taki bini bini saita kira number Ummi kona Gwaggo saima yazo yana tausayin Hajiyan hakanan ba yanda ya iya yamata booking jirgi sukama su Mama sallama da kanshi yakaisu har airport wajajen 8 dan jirgi su 9 ne. 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPİSODE 2️⃣2️⃣ Huuuuhuuuuuu agyara hanya gafa MAMMI HAJIA tazo mana da kayan mata wey no be juju, ba jazz, ba abacadabara ko suddabaru aciki amma kuma aikinshi yafi yankan wuka, MAMMI HAJIA fa tariga tayi suna awannan harkan dan haka ku garzaya aguje kar ayi baku zaku iya shiga whatsapp group nata ta hanyar danna link din nan. https://chat.whatsapp.com/L9xdTKd3MXZJRW8zkAMSqH 22 Hadiza na zaune kan gado wajejen 8 tana kallo a MacBook dinta da aka kawo mata su Rabi Hafsat da Mama suka shigo dakin suna shigowa wani tsalle sukayi suka rungume Hajiya Hafsat tace “barka Ya Hadiza congratulations” dasauri Hadiza da duk jikinta ke ciwo ta turesu tace “zaku karyani me kuke murna haka” cikeda jin dadi Rabi tabama Hadiza labarin komi dasauri Hadiza takalli Anty Jams tace “wai haka? Shine kikazo jiyan nan kikai shiru”? Dasauri ta kallo Mama tace “Mama da gaske wai yar aikin nan ta gudu Hajiya kuma ta tafi” hade giran sama da kasa Mama tayi tace “nidai tunda kin sami lafiya nima gaskiya tafiya zanyi yau” Rabi tace “Wlh Ya Hadiza da gaske barsu Mama da Anty Jams yan Qalallahu wa Qala Rasulu ne su, but Ummi dai tagudu kuma mijinki ne yamata wulakanci jiya yagayama mamanshi ido da ido bazaije nemanta ba ko bikinto shine Hajiya tai zuciya ya tafi yau” wani ihu Hadiza tayi ta dirko ta rungume su Rabi saita fara rawa da waka. “Jarusalema ikayalami eeeee lonolonse…….” Yanda su uku ke rawan daga Mama har Anty Jams tsayawa sukayi suna kallon yan iskan yaran baki abude, Mama tace “stop celebrating other’s downfall duniya juyi juyi ce yau turn dinka gobe nawani, life is like a roller coaster Hadiza, Rabi’a da Hafsatu” Hadiza tace “Mama Allah ne ke sakamin wlh ba maganan roller coaster anan karma yakama yarinyar nan cus taci amanata gashinan da kanta da dauki kafanta ta tafi, the God am serving can never shame me, ni wlh namaji na warke tas tas, tas, azo asallameni wayyyooo dadi Nuri na is all mine again, Nuri kabiyani” ta kankame Rabi cike da jin dadi Anty Jams ta tabe baki. Wajajen 10 Nura ya shigo asibitin da sallama yashiga dakin Hadiza na kwance tana kallonshi tana murmushi cikeda so, dab da gadon yaje yasa hannu yaja hancinta yace “wannan kallon fa” murmushi tayi sosai tace “Mijina yayi kyau ne naga, ina kwana” murmushi yamata yace “close your eyes” dan zaro idanu tayi tace “menene”? Daure fuska yayi hakan yasa tarufe da sauri suma su Rabi duk kallon Nuran suke dumbfounded kofa yakalla yace “come in” Drs da Nurses na asibitin ne suka shigo da katon cake da ballons dayawa a hannunsu an rubuta Happy Birthday Didi akan cake din su Mama da Anty Jams duk murmushi sukayi gabaki daya kowa ya manta yau birthday nata har ita kanta ta manta, yakalli Hadizan yace “open your eyes now” ahankali tabude kawai aka fara waka. “Happy birthday to you, Happy birthday to you, Happy birthday to Hadiza Happy birthday to you…..” fashewa da kuka sosai Hadiza tayi tana kallon Nura kaman ta tsaga jikinshi tashige takeji karban cake din yayi yadaura akan cinyanta yana mata wani kallon soyayya yace “happy birthday Didi, oya blow you candle” blowing candle tayi akahau ihu ana tafi ta yanka cake din red valvet tace “wowww my favorite Thank you Nuri, I love you, thank you all” takalli sauran Drs da Nurses din tamusu godiya duk akacici cake din adakin aka watse Hadiza sai kallon Nura take she can’t believe Allah yabata miji dake sonta haka yake kuma son yaransu juyowa yayi suka hada Ido ya harareta yace “you are 33yrs yanzu, no more tsiwa da rashin ji da stubbornness” pledging tayi tace “nadaina I promise” Mama ta tabe baki tace “Allah sa” fuskanta ya shafa yace “bari nadan leka office kinason wani abu” girgixamai kai tayi tace “saika dawo Allah tsaremin kai” lumshe mata ido yayi yace “Ameen”yafice. Mama tace “kinyi sa’an miji Hadiza saidai kice Alhamdulillah I hope you will change for good wlh kika rasa Nura kin rasa miji har abada” Anty Jams tace “nama Majal magana nabiya kudi nama tura mata number ki zata saki group dinta na matan aure mai suna Somach dan ubanki saura kada ki natsu ki koyi abubuwa you are 33 yanzu Allah ya chanza ki, namiki order wasu kayan mata from MAMMI HAJIA, shedanun cikin magungunan ta namiki order da HQ ADDICTION, RUWAN BAGAJA da OGA MUST SALUT, gobe tace zatamin delivery tun anan asibiti zaki farasha sabida yabi jikinki” murmushi Hadiza tayi tace “thank you Anty Jams dina don’t worry this time I will make you all proud of me, dagajin sunayen magungunan nan zasu tsula tsiya” Anty Jams tace “dole Nura yaga chanji wlh” **** Yau Hadiza ta cika one week a asibiti yau aka sallamota suka dawo gida yaranta sai murna suke gobe da sassafe yan uwanta zasu koma kano girke girke suka mata daban daban aka lollada a freezer da uban stew kusan cikin roban fenti duk wani aiki dake gidan sun mata dudda babu wani abinda ke damunta ta warke tass though tanata appointed da psychologist daya ga wata mai zuwa but she’s fine sai uban kayan mata MAMMI HAJIA take sha. After Magrib yashigo gidan duka akaci abinci tare yakara yin sallama da yan uwanta yawuce masalları sallan isha’i shida Aman. Wajajen 9 suka shigo gidan yana rikeda Aman dayayi bacci, bakowa a falon sama yawuce yaje dakin Aman din ya kwantar dashi sannan yawuce dakin Hadiza batare daya kalli dakin Ummi ba Hadiza na kwance kan gado tasaka wani arnen rigan bacci pink shara shara, wani kalan kallo Nura yamata yana maida kofan yana rufewa murmushi tamai tace “nayi kyau”? Tai wani juyi agabanshi yace “kin tashi kaina Didi” wucewa yayi yarage kaya tabishi da kallo kaman zata hadiyeshi sannan yabude bayi yashiga dan ya watsa ruwa shiru tayi tana tuna karatın da Majal tamusu kan wanka tareda miji na kara love, kayan jikinta tashiga cirewa ahankali tawuce bayın tabude ahankali Nura na kasan shower kaman daga sama yaji an rungumeshi tsantsan ijiyan zuciya yasauke murya Chan kasa yace “Didi” murmushi tayi cikin yar karaman murya yace “I didn’t get the chance to thank you properly kayi dawainiya dani sosai this past few days not to even talk of kudaden daka kashe for my cardio test da tp to and fro na yan uwana suzo, the suprise birthday and everything, u are indeed my soulmate, Nuri I love you over” wani kalan juyo da ita yayi gabanshi yabi jikinta da kallo ahankali yace “kome namiki kaina namawa Didi me and you are one!” Zata sake magana yawani fizgota jikinshi yana mannata bango manna mata kiss yayi a forehead ya manna mata a hanci kafin ahankali yasauke bakinshi kan nata yafara kissing nata tana maidamai da martani, Ummi ne tafado mai rai he just remembered how she loves kissing him is like whenever it comes to kissing she do most of the work kaman zata cinyemai baki. “Nuri!” Hadiza takirashi bakinta cikin nashi ganin ya tsaya and he’s lost in thought, dasauri ya kalleta yacigaba da kissing nata yana budemata kafa he knacked Hadiza well cikin bayin nan to his biggest suprise batai complaining yajuyata nan ko chan ba full cooperation tanashi, he can’t lie he enjoyed it takara dadi sama da yanda yake jikinta and she’s so tight sosai yau and so warm maganin Hajja mammi yayi aiki, itama Hadiza unlike her the sex yamata dadi bata taba sanin Nura at clocking 50 will this good ba, what a rude f*cker, wanka sukayi suka fito suka hau gado kashe wuta sukayi ta rungumeshi da sauri tareda kai bakinta saitin nashi tace “I love you Nuri” ahankali yace “I love you too Didi” daura kanta tayi kan kirjinshi yana rubbing bayanta ahaka bacci yayi awon gaba dasu. Washe gari by 8 suka wuce yara dama tun safe suka tafi school Hadiza takalli Nura daya wuce sama tace “bazakaje aiki ba yau” yana murmushi yace “sameni asama today is all yours ba inda zani” murmushi tayi sosai tabiyoshi sama harya kwanta kan gadonta da gudu taje tahau kanshi yace “shikenan zata karyani ke bakisan na soma tsufa ba”? Tana turo baki tace “kai Nuri shairi har wani kiba gareni kuma ni banga tsufan dakake fadiba kamafi wasu samarin iya cin mace” dan kanne mata ido yayi yace “wlh shinakeso ma yanzu kinyi dadi sosai jiya, ride me Didi dagani sai ke gidan” ba musu kaya sukahau ciccirewa juna Hadiza tahau riding nashi dan yanzu bata gardama one two three tagaji sai kawai Ummi takara fadomai arai dasauri yakauda tunaninta ya kwantar da ita yahuayi, ranan wuni sukayi suna more rayuwansu yanda kasan sababbin Amarya da ango. Washegari Yau dukansu zasu aiki Nura shiya shirya yaran da kanshi, Hadiza ta sauka kasa hada musu breakfast. Nura na sama Aman takalmin makaranta yace “Dady har yanzu Anty Ummi bata dawo ba”? Kallon Aman Nura yayi dasauri, Amal tace “Dady I miss Anty Ummi so much” sai kawai yaran duk sukai kaman zasuyi kuka dasauri Nura yace “don’t worry kwanan nan zata dawo okay, muje yanzu Momy ta gama breakfast muci okay” wucewa kasa sukayi atare duk sukai breakfast din mota yazo Nura yafita yakaisu Hadiza ta tashi yace “lemme shower Nuri natafi” dasauri yakalli dinning da kitchen din daya hangi wanke wanke dayawa a sink yace “what about the plates din baki wanke ba the kitchen is looking dirty Didi” Dan tsayawa tayi tareda yatsine fuska tace “bazan wani dadeba zan dawo kasan online sales din dazanyi has been on hold sabida rashin lafiya na, yau kawai zanje ne muyi sorting out everything new kayan danai order zasu iso next week” ahankali yace “okay nine wuce” daga sama tace “adawo lpy” tashi yayi yafice zuwa office Musa ya tarar a office dinshi yace “waikai tunda kayi Amarya ka zunda mu” dan tsaki Nura yayi yasami waje ya zauna saikuma yayi shiru tareda daura hannunshi saman kanshi dasauri Musa yace “lafiya”? Kaman Nura bazaiyi magana ba yace “Ummi tayi zuciya tabar gıdana ta tafi garinsu” cikeda mamaki Musa yace “mene? Kai dalla banson this expensive joke, yaushe kukai auren dahar zatai yaji meya faru”? Gayamai komi Nura yayi Musa yace “haaabaaa Nura, haba kaikuwa dudda ina namiji koni banji dadi ba, Allah sarki Ummi the poor thing must’ve felt all alone wlh dole ta tafi yanzu dai yaushe zaka je daukota dan is obvious kayi kewanta” tabe baki yayi yace “ni kewanta da danedai zan gayamaka eh, yanzu ko tayi shekara ma karta dawo, gida biyu maganin gobara, ni zatama zuciya, haba yau idan inaso zan iya auro mata uku akanme zatace zatamin zuciya babu wani dalili mai kyau, kai kasanni bana batawa mutum rai hakanan maisa bazata min uzuri ba, takari zamanta baxaniba” sosai Musa ke kallonshi kai tsaye danshi yafi Nura iya duniyanci yace “saketa in aura Nura dan Allah!”. Da sauri Nura yakalli Musa gabanshi yawani fadi danjin maganan yayi kaman saukan aradu sai kawai lips nashi yahau rawa yama kasa magana sai kallon Alhaji Musa yake dake kallonshi kyur ba kunya ba tsoron Allah, cikeda kara gasgatama Nura yace “wlh Nura da gaske nake yoo idan naboye maka zan boye ma Allah ne damukaje bikinka kasan yanda naketa nanatawa azuciyana inama nine kai, inama nataba zuwa gidanka naga Ummi, from the way you are talking Nura bakason yarinyar nan Hadiza itace matarka da Allah yabaka, ku biyun kun dace da juna, yarinyar nan Ummi ka aureta ne kawai to pepper Hadiza kadawo da ita hayyacinta, tunda bukatanka yabiya Hadiza tadawo daidai tadaina gasaka ni ka taimakamin kasaketa na aura wlh wlh ina bala’in son Ummi Nur……” “get out!” Nura yadakama Alhaji Musa tsawa dayasa Musa yace “waikai lafiya komi ke baka haushi kwanan nan, naji zan fita amman dan Allah bani number ta, ban number Ummi” yamikama nura wayanshi wani kalan zabura Nura yayi yatashi kaman zaki idanunshi sunyi jazur yawani kama gaban babban rigan Alhaji Musa cikin tsananin bacin rai kaman zaiyi dambe da Musa yace “matar tawa kake cemin nasaka kana sonta zaka aura” bawai yaji haushi abinda Nura yayi bane amman yasa hannunshi tacire hannun Nura daga gaban babban riganshi yace “Nura bari kaji ni bazan rabaka da matarka ba kuma bazan taba neman matan aure ba kai kasan wayeni bana irin harkan nan, I’m simplying telling you tunda tagama amfanin dazata maka baka sonta yanzu, kasaketa ni zan aureta dan wlh Ummi tamin right from day one dana ganta, kuma ni auren so da kauna zan mata nabata gata da komi ba irin selfish auren dakayi da itaba” “to baza’a saketa ba!” Nura yayi maganan yana tura Musa, Alhaji Musa yace “kana saki kaman na aure yasin nidai tunda yanzu baka tunani da kyau kaga tafiyata zan kiraka kahuce karka manta dan Allah kasaka na aura! And try send me her number!” Bugo kofa Nura yayi azafafe. 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣3️⃣ Alhaji Musa yawuce abinshi ganin yanda Nura yabugo kofa behind him, azuciye Nura yakoma kan kujera ya zauna tareda da fuzar da iska yadaura hannunshi akanshi, he’s even angry da kanshi why is he getting worked up all because of sarkin zuciyan nan eh? Imagine taje gida ma Gwaggo kotadan kirashi aji meya kawota gida an barshi an zubamai ido shi zasu wanawa zuciya, dago kanshi yayi yay punching table din yawani mike tsaye tareda kwasan wayanshi da car key nashi yawuce yafito daga office dasauri secretary nashi tace “Sir ina zaka kamanta da meeting naka by 12PM ne” azuciye Nura yace “cancel it” baima kara bi takanta ba yawuce yasauka kasa yaje yashiga motanshi yaja zuwa gida, baimasan takamaimen dalilin why he’s coming back home ba, bude kofan falon yayi yashiga ciki ya tsaya anan mini polour yana kallon cikin dakin da ba’a gyaraba ga tarkachen su Aman duk afalon, dinning duka plates dasukaci abincin safe nawajen, falon babu wannan kamshin turaren daya sabayi na wuta, ahankali ya sauke ijiyan zuciya yacire takalmin kafanshi yawuce yashiga cikin parlor ahankali yake tafiya yanabin ko’ina da kallo yawuce kitchen ya tsaya daganan bakin kofa yana kallo, wajen burners na gas duk spill na oil, kwayoyin shinkafa, menene, menene, ga pots daban daban kan burnes din some properly closed while some half closed, sink ma plates sun cikashi tap, rungume hannunshi yayi akirji ahankali sai kawai yaga Ummi tajuyo takalleshi tanamai murmushi da spoon na girki a hannunta, runtse idanunshi yayi dasauri kafin yajuya yana bude idanunshi yawuce sama ahankali, saman ma same thing toys din su Amal sunfi guda 100 scattered dasu, building blocks ko’ina ga balls da some pieces na toy kitchen din Amal anan falon saman, wucewa yayi yasami kujera daya ya zauna ahankali yakai yayi shiru duk wanda yasan Nura yasan he’s not happy, kusan 5mins yayi ahaka sannan yajuyo yakalli dakin Ummi yakai kusan 1min yana kallon dakin da har yau bai shiga ba rabonshi da dakin tun randa yafito yakai Hadiza asibiti, mikewa yayi ahankali yawuce gaban dakin kafin gently yasa hannunshi yabude kofan sanyin AC dan Ac a kunne dakuma kamshin turaren ta dana daki sukamai sallama, deep down he wish zai ganta tazo dagudu ta rungumeshi amman dakin wayam ba kowa sai wata yar rigan baccinta red dake kan gadon da roban mentos chewing gum. Yadade tsaye abaki kofan yana kallon dakin kafin ahankali yashigo cikin dakin yamaida kofan yarufe yafara takawa ahankali yawuce gaban wardrobe nata yabude duka kayanta na wajen bata taba komiba, komi nata agyare suna kamshin turaren wuta, bayinta yawuce yabude komi agyare kal saidan pant nata red dake makale a hanger data wanke, yadade yana kallon pant din hadiye wani abu yayi awuyanshi, ahankali yashiga cikin bayin yasa hannunshi yaciro pant din yana kallo tareda dan lumshe idanu yadaura fuskanshi kan pant din dake kamshin detergent yakai almost 1min ahaka sannan yacire yabi bathtub na bayin da kallo komi na ranan dasukai wanka awajen tare na dawomai, ijiyan zuciya yasauke yafito daga bayin tareda jawo kofa yarufe wardrobe nata yabude ya linke pant din ya ijiye yazo gaban gadon yadauki rigan baccinta shima ya linke yazo yasa cikin wardrobe din ya kulle, yazo ahankali ya tsaya gaban gadon tareda folding hannunshi akirji yana kallon gadon he’s just seeing Ummi da shi akan gadon having a devine and soulful sex, the way she rode him that day tabashi the craziest and dirtiest ride of his life was just spectacular and that massage was titillating, Ummi made him felt like a man after a very long time the gurl is licentious cus wen it comes to sex yarinyar is tarbiyaless, the level of her sexual strength just match his, bata minding dik yanda zaiyi swinging and flipping nata, despite where she’s from but she’s so good and a freak in bed she’s just gamy. Kaman asiri yakasa manta yan abubuwan datamai he’s just craving for touches and smooshes nata, he’s just longing for the way she dominated him that day and used his body kaman Guinea pig, funny enough da kiss din datakemai yake kewa so badddd. Wani kalan fadawa gadon yayi yajuyo yana kallon saman dakin breathing fast fast yakai hannunshi yana kwance belt din wandon dake jikinshi trying to free kanshi cikin wani kalan muryan wanda baya hayyacinshi at all yace “hau kaina kicini Ummi” wani kalan lumshe idanu yayi yana budesu kadan kadan stroking his hard joystick daya fito dashi waje yace “yes Baby ahhhh Ummi zaki kasheni ahhhh, ooh shitt, ooouchhhh” “Nuri!” Kaman daga sama yaji muryan Hadiza takirashi firgigit yadawo hayyacinshi yana sakin joystick dinshi dasauri yana juyo da kanshi da idanunshi da sukadan chanza kala suka hada ido da Hadiza dake tsaye gaban kofan dakin tanamai wani irin kallo, wani takaicin mummunan tsaki Nura yayi feeling angry with kanshi, what is even wrong with him abinda baitabayiba all his life did he just do it picturing that girl? Tashi yayi dasauri yana maida abinshi ciki dataki kwanciya yana gyara wando batare daya kalli Hadiza ba, asanyaye Hadiza na kallonshi tace “Nuri are you okay? Kasan tundaga ina nakejin muryanka kuwa? Tundaga downstairs? Soapy kakeyi”? Wani kallo Nura yamata dasauri yace “tunda kika sanni kintaba ganin nai abin nan banyi da ba yanzu ne zanyi” kara gyara riganshi da wando yayi yace “zan koma office” yazo ta gefenta zai wuce karaf Hadiza takama hannunshi tanajin wani mugun ciwo da bakin ciki aranta kaman ta shakeshi tace “Nuri what has gotten in to you? Uban me yarinyar nan tamaka? Why are you even in her room? Nace ubanme tamaka? We had sex shekaran jiya da night still munyi da safe, munyi last night, munyi yau da asuba and I caught you kana this thing me yarinyar chan yar aikina tamaka Nura? Gindin lu’u lu’u gareta haka haryakai kana neman cin kanka am I not enough for you Nura? Me ban makaba? I’ve changed? We had a very juicy sex this morning before subhi, u enjoyed it every bit ma kuma, mena rasa tell me? Is that karuwan yar aikin tawa better than me da saikayi amfani da kank……” “Hadiza!” Nura yakirata azafafe tareda nunata da yatsa yace “mind your language! Don’t ever call anybody sunan dakika fadi just now, and karki kara alakantani da wat u just said, whatever you just see now is not abinda kike tunani, I agree I was lost for some moments but is not abinda kike tunani, kuma ai bantaba gayamiki u are not enough for me ba, I have my personal life Hadiza don’t just intrude” Nura yayi maganan dadan fushi zai wuce Hadiza tasha gabanshi tareda bude hannu sideways tace “why are you soo angry? Did you just said kanada personal life what am I to you? For God sake I am your wife! Mother of your only kids aduniyan nan, Nura wlh u insulted me with this dana kamaka kanayi and I demand to know why? Am I not enough for me? Da me yarinyar nan tafini? Nura why are you hurting me ni Hadizan ka mena maka haka? Nura na chanza, na chanza, na chanza so akanme zaka shigo dakin yarinyar nan data gudu ta barka kana mammatse gabanka saikace tuzuru? Our lives has always been just me, you and yaranmu this is not you Nura, I don’t recognize you anymore, Nura muna zama 2months bamu nemi junaba and both of us are fine, this is tun farkın auren mu haka muke, gabaki daya sex baya gabanka so tell me wat am I lacking Nura? I demand to know tell me!” Tai maganan shouting sosai kaman zata tada gidan idanunta sunyija ihun dataji yanayi ranan na dawo mata fresh azuciya, kallonta Nura yayi strictly yace “Hadiza don’t start this war dakike shirin farawa you just got back from hospital, I’ve never complained cewa u are not enough for me, like I said a asibiti ni da ke mun rufe chapters din da mun bude fresh one, so just drop this topic ki tashi daga gabana nakoma office, I enjoyed wat were having this days saisa nakasa kyaleki kihuta every minute ina kanki so kitashi ağababa nakoma office” “Wlh bazan tashiba Nura” Hadiza tai maganan cikeda masifa tace “mesa maza munafukai ne ku! Nura wanda bai sanka ba will think u are a saint but u are an evil and a very wicked man” Hadiza tayi maganan hawaye na fitowa daga idanunta tace “nakamaka doing this thing calling sunan makiran nan, now am asking you kafadamin abinda nake lacking nima namaka sabida k daina tunata ka kasa, bakin ciki kake namaka ba itaba? Kafinson na dawwama a square one? You don’t want me to please you kafison ita to please you huuun? Kai wani irin munafuki n…..” tasss! Nura ya dauketa da mari dayasa Hadiza tai baya zata fadi da sauri ya fizgota da hannu daya ya nunata da hannu daya yana kallon kwayar idanunta yace “enough Hadiza! I am not stupid nor am I a fool kinajina!” Yamata ihu da saida ta firgita a hannunshi dan kaman zai rufe ta da duka, yace “I am tired, mata daya na zagina daya namin zuciya nagaji!” Yasake ihu yace “kinata tambayana me kike lacking kin taba kama gabana kin sha for 10-11yrs today?!” Yayi ihu yace “you are zero point zero point zero plus zero minus zero multiply by zero in sex!” Wani girgiza Hadiza tayi tana kallonshi idanunta sunyi jazur, yayi ihu idanunshi sunyi ja yana kallonta acıkın ido yace “I hate hurting you Hadiza! I hate hurting your ego, why do you always push me ni yaronki ne dazaki titsiyeni saina fadamiki why nake abinda kikaga inayi ina ruwanki? Da jikinki nayi koda nawa? Listen if you want to kill yourself do it kije ki amsa Allah cus I’ve tried my best for you, I hate how stubborn you are, I hate myself dana kasa cire fitinanniyan mace irinki araina haryau, nagaji Hadiza, nagaji da draman ki da draman kowa ma nagaji, sabida su Amal nake zaman gidan nan kika dameni zan bar miki gidan nan gabaki daya wlh nagaji!” Yamata ihu a fuska tareda sakin hannunta yawuce fuuuu kaman zai fasa staircase da dirin tafiyan shi. Please readers listen to me with open mind, wallahi wallahi bana supporting kowa in this book, sunan littafin nan fa MATAN da question mark ❔ ko MAZAN shima da question mark wato alamun tambaya ❔ Dawuya kaga novel tittle mai question mark, duk inda kagani you should know cewa littafi ne da the best thing for you is to read it without picking side just read it to learn. This book Ina portraying life of family dakuma familyn family, kowa nacikin book din nan is there for a reason, Nura’s family, Hadiza’s family, and Ummi’s family as well. Men can act funny, and sometimes men are the origin of major issue na aure. Believe me Hadiza is acting daidai ita daidai yanayinta, same with Ummi, kowa nada ways na nuna anger nashi, look yanzu Hadiza ihune da zagi nata idan tana fushi most mata haka muke, Ummi zamu iya cewa zuciyane nata, believe me tafiyan datayi bisa karamin misunderstanding haka idan big misunderstanding yafaru yaya kenan? Kowafa nada way of showing anger, wasu ma fashe fashe suke na kayan gıda idan mijinta yabata mata rai, wasu kuma dukan yaranta sunan su pepper soup ranan😂 Shikuma Nura look at him shima yadebo da zafi matarsa Hadiza bata sabamai zuciya ba Ummi tayi yace bazaije ba girman kai, do I look like ina supporting any one of them??? Aure is complicated! No marriage is FREE of issues that one na lie! Kudai Allah ya kyauta, please read and learn from side na Hadiza, na Ummi dana ma Nuran as well. And Sex listen Sisters, Kayan mata na kara ni’ima dadi da sauran su, but shi good sex is skills, Hadiza tasha kayan matan MAMMI HAJJIA which yayi aiki ko Nura yafadi takara dadi and tight problem nata is the skills and technique that knowledge da willingness na son tayi with passion, and naturally she’s not a sex freak which akwai mata dayawa da basu damu da sex ba like Ummi. Matan kauye yawancin su nagaya muku na son harkan bindi kuyi tambaya kuji. I said my own so just chill🥰 Now tell me so far so good with all the gbas gbos are you enjoying MATAN KO MAZAN?? RATE THE BOOK ⭐️ ⭐️⭐️⭐️⭐️ 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣4️⃣ Yau nazo da gangariyan rahoto wato PRACTICAL CHINA IMPORTATION class💃💃 Ga inda zaki koyi asalin ilimin saro kaya daga china, za’a koya miki ko dubu 20 kikeda shi zaki iya fara saro kaya Wayyoo Allah na, babu wani dogon zance kuzo mu shiga WAITLIST din nan tare💃 Danna link ki shiga group din waitlist https://chat.whatsapp.com/FIKdtOLn4vjGOQ1bHuI9l0 24 Sauka kasa yayi zuciyanshi na masifan tafarfasa yabude mota yashiga ko gaisuwan da maigadi kemai be iya ya amsaba yaja motan shi sabida yanda ranshi ke soyuwa yanar gidan, he’s just angry da kowa, Hajiya tunda takoma kano taki daukan wayanshi, koya kira Meena yanason magana da ita bata amsa tace agayamai idanba ya nemi Ummi bane he shouldn’t bother about talking to her, ga kuma Ummi dazata kama tabar gidanshi tanamai zuciya akan abinda baitaka kara ya karyaba dan shi har yau baiga wani takamaimen abu dayamata ba, kuma takama takashe waya irin she doesn’t even wants him to look for her, she’s done dinnan, saikuma Alhaji Musa yana wani gayamai ya sake Ummi shi zai aura sabida an gayamai shi auren dan ya saketa ne yayi, now kuma Hadiza ta tsareshi ta titsiyeshi kaman danda ta haifa saiya mata bayani mesa yayi abinda yayi, why is everyone doing yanda yaga dama dashi he’s just so tired, mesa the peace he’s yearning for at this age yakasa samu? Why? Mesa stubborn women ne suka cika rayuwanshi? Da kyar ya iya kai kanshi office yawuce sama yashiga office nashi yama rasa ina zesa kanshi yaji dadi. Yanda zuciyan Hadiza ke bugawa zaka dauka kararrawa ake bugawa aciki, hannunta har lokacin nakan kuncinta da Nura ya mata, bakinta kuma asake tabishi da kallo har saida taji tashin motanshi sannan tawani zube zaune awajen, kuka ke zuwan mata sosai amman tahana kanta no bataso tasake zubarma da wanda yamata bakin zagi haka, yau itane Nura zai hurting nata haka for the second time dan auren Ummi was first, wannan kuma nabiyun, ita Nura zai kira zero! Ita, a Cinderella, Nigerian kardashin, business mogul queen, Oga wife like her, yasan how many online business vendors ke shishige mata, all matan abujan nan da gangan suke zuwa shagonta abaje bajinta ayi shopping just sabida aburgeta tayi kawance dasu, infact duk randa take shago anmafiyin ciniki, wani kalan gyarane batayi, saloon treatment daban daban, even a sex din this days she’s trying alot, inhar namiji zai ciki yakawo kuma how dare he calls you zero? Da ace Nura tun farkon aurensu ya nuna yadamu da sex he wants it da babu yanda zatayi dole ta dinga bashi, she’s not lying but itada Nura nazama gida daya for 2months abu bai shiga tsakaninsu ba, wani kalan maita yarinyar nan tazo tazuba ajikin mijinta cus she don’t recognize Nura anymore, ita Nura zai daga hannu ya ketama mari? Why is he so angry? Bata taba ganin Nuri na wannan fushin masifan ba, metamai dazai mata kalan marin nan??? Parking motan dataji anyi yasa ta zabura ta mike tayi stairs tasan shine halan yadawo ya lallasheta ne daidai tana karasa saukowa kasa daidai ana bude kofan falonta ana shigowa. Baraka da Zeena ne suka shigo rikeda wani hamper na snacks da fruits aciki suka hada ido dasauri wani irin kunya Hadiza taji ganin kawayenta ne ga gidanta kacha kacha ga jan idanunta maybe akwai hawaye aciki dasauri daga Baraka har Zeena suka karaso cikin falon, Zeenah tayi wajenta da gudu tana bude hannu tace “oyoyooo my Sick baby sannu, wlh nida hubs munje Maldives ne ai I told you about the birthday trip dazaimin saisa banzo na gaidaki ba I just greeted you a IG da naga kinsa, jiyan nan nadawo yanzu ma shago mukaje akace kin dawo gida nacema Baraka let’s go gidanki, sannu Haddy, how are you feeling now”? Murmushi Hadiza ta kakalo tana kallon Zeenah dataci gayu tasha gwalagwalai tayi kyau takara kiba sai sheki take, tace “na warware tass nida harnayi resuming zuwa shago ma” dasauri Baraka data ijiye hamper anan falo ta taho wajen benen tace “sannu Hadiza Allah baki lpy, ya duk na ganki wani iri haka” tai maganan tana mika hannunta dasauri zuwa kumatunta tace “an mareki ne naga kaman shatin hannu” dasauri Hadiza zata juyar da kanta Zeenah dabata luraba takama habarta tana zaro idanu tace “what happen to your face? Kinga hannu shaaaa a fatan fuskanki yayi jazur sabida farin fata, who slapped you”? Wani kalan fizge fuskanta Hadiza tayi tace “dalla kubarni waya isa ya mari Hadiza aduniyan nan are you guys for real? Zoku zauna bari nakawo muku drinks” tawuce zata tafi dasauri Zeena takama hannunta dan she’s just like Hadizan saisa itace best friend nata. Tace “Besty kaman ya bari ki kawo mana drinks I don’t understand, in your own house kene ke serving guest drinks ina yar aikin ki?” Zeenah tamata tambayan kai tsaye dan cikin duka mutanen Hadiza banda yan uwan ta najini babu wanda ta fadiwa Nura yayi aure dan abin kunyane agareta, zatai magana Zeenah tace “tell us we three are childhood friends ku munma juna dariya kanmu mukamawa remember yanda mukema Baraka fada, what’s happening? Who slapped you haka a fuska? Sannan ina yar aikin ki? Why is your house so dirty haka? Look at falon nan see dinning why is everywhere so scattered and disorganized, I don’t even wanna talk about yanda kika rame cus I wanna believe rashin lafiyan dakikayi ne yasaki kika rame but who slapped you this hard eh”? Baki Hadiza tabude zatai magana kun gane irin kukan nan da baka bashi izinin zuwa ba amman kawai sai yazo without permission shiya kufce mata da sauri Zeenah ta yarda jakanta tace “ohhh no come here sweetheart it’s okay, it’s okay, who hurt my Didi this much? What’s going on Didi talk to me, Baraka zo” dasauri Baraka ta zo dukansu suka rungume Hadiza kafin Zeenah tace “muje sama mu sauna kawo mata ruwa Baraka” gyadamusu kai tayi Zeenah tawuce da crying Hadiza sama Baraka kuma tawuce fridge ruwa a dauka suka wuce sama, Zeenah tabude ruwan takai bakinta tace “sha Hadiza” kadan ta kurba ta ijiye ruwan, ahankali tace “menene Hadiza talk to me who slapped you”? Cikeda Jin nauyi da kunya but sun riga sun kamata babu yanda zatayi tace “Nura ya mareni!” Daga Zeenah har Baraka zaro ido sukayi cikeda mamaki Zeenah tace “Nura yamiki wannan kalan marin?” Gydamata kai Hadiza tayi tana fuzarda iska, rai abace Zeenah tace “baki suing nashi for domestic abuse ba are you okay Hadiza? Your husband is abusing you haka, maisa baki daukomai yan sanda ba”? Dasauri Baraka tace “haba Zeenah wani kalan yan sanda kokuma tayi suing nashi sabida just this one time mari is not something dayake faruwa kullum shekaransu nawa tare yataba marinta ne” cikeda masifa Zeenah tadagama Baraka hannu tace “kinga just keep quiet and allow me talk to my friend ke dama kin saba tolerating all sort of trash daga mijinki saisa he doesn’t respect you, Hadiza and you are two different people, she knows her rights unlike you akanme, akuma kan wani dalili Miji zai kama yana taba lafiyar jikinta tai shiru look at her precious face, kinsan da kasan waje ne kalan hukuncin dazaihau kan Nura kuwa look at her face for crying out loud yadauka jaka ya auro ko tumakiya, yadauka bakida gatane am calling my lawyer inama jakana” ta jujjuya ganin bataga jakanta ba yasa ta mike tawuce kasa rai abace, Baraka ta kalli Hadiza dake goge kwalla tace “yanzu zakiyi suing Nura sabida ya mareki Hadiza? Me aciki dan Nura ya mareki yana marinki da ne? Why are you and Zeenah like this eh? Nura fa baban yaranki guda biyu ne shi zaki maka a kotu? Ko darajan yaranku bazaici ba”? Shiru Hadiza tayi daidai Zeenah na karasowa tace “say whatever you wanna say Hadiza is not you and can never be you, duk matan dazata zauna miji na dukanta anytime dayaga dama jakace kuma yar akuya, kuma dakikiya ni Zeenah nafadi haka, and idan tabari wannan to slide to Nura yadingayi kenan kalleni nan Hadiza” Hadiza takalli Zeena tace “ask Baraka dazu da dasu Hanna da Saudat da some members na meeting dinmu zamuzo fa but mukace bazamu iya jiransu ba, da dasu mukazo da bakiji kunyan duniya ba? Da gulmanki saiya zagaye Abuja fa ana mijinki na dukanki, waye Nura? Duka kudin gudanawa gareshi da he feels zai iya miki kome yaga dama haka, waye ubanshi? Shida kudinma nemansu yayi ba haihuwanshi akayi aciki ba, look at you Hadiza yazaci idan kin rabu dashi zaki rasa mijin aure ne? Koya dauka shi Autan maza ne? Kinmasan how beautiful you are kuwa Hadiza? Wlh yarabu dake saikin sami mijin dayaci ubanshi akomi, just like me yanzu minister nake aure, da Bala yafara dukana dayaga I know my right namakashi a kotu ya biya ai yagane koba komi na batamai clean record nashi, sunanshi is registered under domestic violence yanada record dazai bishi ko’ina, sannan na barshi, u were there for me lokacin look at me yau married to minister dakeda mata biyu nine ta uku but nice yar gaban goshi, ki watsar dawani soyayyan nan ki yaki Nura fa, wlh kuka rabu da Nura zaki sami mijin dayaci ubanshi akomi barinma yanda aka sanda ke a abujan nan da business naki haba, kina daga cikin top housewives of Abuja fa dake representing Abuja who d f*ck is Nura? Take action against him now kafin ki zama Baraka part two” rushewa da kuka Hadiza tayi tashiga fadamusu duka abinda ke faruwa tundaga auren Ummi, mutuwan zaune sukayi sai kawai Zeenah tafashe da kuka tace “Baraka let’s go tashi mutafi Hadiza bata dauke mu as family ba, Baraka koda you were going through something, dudda bazakijin shawaran mu but sharing heals right and we are always there for you cus an zama daya we never abandon you” Baraka tace “kwarai, I don’t agree with ways naku but I’m always grateful to have the two of you as friends dina I know sometimes kumun dariya kuji haushina kaman zaku daken but baku taba kai magana ta waje ba it remains among us, and both ke da Hadiza always helps me financially, idan something come up a meeting na association namu zakumin anko baku taba bari an gane inada wata matsala ba kallonmu ake dukanmu ukun daya, I know kuke ganin abu ya bambanta dani but friendship naku is genuine, Hadiza why will you be going through something like this bazaki fadamana ba”? Cikin kuka tace “zakumin dariya barinma ke Baraka I remember yanda nake miki dariya ina kiranki wawiya mara wayau, that’s why” girgiza mata kai Zeenah tayi tace “the three of us are one saidai sauran kawayen mu su mana dariya but never us Hadiza, Nura babban shegen dan buhun uba ne, kici uwarsa wlh yagane ke ba kanwar lasa bace, being a wife doesn’t make you a slave, shi wani kalan mara imani ne, look at how big this house is, taya zaki fara kiyi shara kiyi mopping kiyi wanke wanke ki tattara kayan yara ki wanke a washing machine ki shanya, kiyi kuma nashi, kiyi girki ki wanke plates, u are working class woman fa your business needs you naaa Hadiza this is pure wickedness Nura bayason ci gabanki he wants your business to crumble saisa yakeso kina all those aiki ke kadai without help how will you manage? Ko kula da yara aka barki yimusu wanka feeding them, homework getting them ready for school is it easy? Kananun yara gareki fa 4yrs and 2yrs how will you manage”? Ahankali Baraka tace “ni yarana hudu nike komi” Zeenah tace “you are not working so karki hada kanki da Hadiza you are housewife” takalli Hadiza tace “clean your tears kada ki kara wasting hawayenki akan da namiji barinma wanda yayi betraying naki kaman Nura, wlh da yarinyar nan nanan yau da saina sa an kulleta a barrack su mata jina jina a kwakule tsinanniya, ita harta isa ta yaudareki ta aure miki miji suna cin gindi da daddare suna ihu suna nema su kasheki kuma kika zauna, are you mad Hadiza? Yau idan zaki mutu let’s assume baida wata matan ma kafin 40days wlh Nura yakara wani aure ballema ya auri yar aikin ki shagalinsu zasuyitayi abar family ki da kuka cus yaranki bayi zasuyi ba they’re still very small yan uwan ki kawai zasuyi bakin cikin ki Nura, Nuran uban meyeshi kin nanama kanki sonshi mugun mutum is he the only man on this earth? My dear clean your tears” goge hawayen ta Hadiza tayi tanajin karfi na zuwan mata wannan ne kalan shawarma dataso Anty Jams tabata amman bata bataba, sai shawaran dayasata cikin wahala kawai all this while. Zeenah tace “Hadiza it seems you are lost kin manta waye ke lemme remind you girlfriend” Zeenah na kallonta tace “Hadiza you are a strong independent woman wacce ko da namiji ko ba namiji you can live your life and survive on your terms, you are a feminist Hadiza!” Wani karfi Hadiza taji yashiga jikinta, Zeenah tace “idan zaki mutu die of normal course badan namiji ba, a man is too small yabaki ciwon zuciya! Ke with ko without Nura you have you can have a better life, kinada booming business worth millions of naira, you have cars, kinada yara tell me mekike bukata awajen Nura da zai dinga marinki bayan yaci amanarki yana miki tinkaho”? Ahankali tace “babu! I can do everything for myself, I can live my life yanda naga dama, I have money to sponsor any desire na, inada gida dana siyama kaina a kano” Zeenah tace “good now kin soma dawowa, ke Nura ya auran miki yar aiki baki tadamai hankali ba kika cigaba da zama dasu ana cusa miki bakin ciki, yarinya na kada takashi agabanki left and right ba kunya ba tsoron Allah in your own house, gidanki fa Hadiza asiri Nura yamiki ko yamiki rufa ido da rufa baki ma duka? Ya taushe miki bakine da bakici kutumar buhun bura ubansu ba dagashi har yar aikin kihanasu kwana agidan” ahankali Hadiza tace “looking back wlh I’m regretting daban tadamai hankali ba, Zeenah banmasan meya shigeni ba those days, bansan wani kalan wayau Nura yamin ba kawai yadinga kwanciya dani yanamin some things that I can’t even explain, bansan wani kalan brainwash and mind wash yamin ba but anyi an gama, yashani kuma na warke, Is time to let him know know that I am still that Hadiza kuma daidai nake dashi, first and famous bari na samo yan aiki dan koni I hate dirty, zan dauki yan aiki guda hudu, 2Nanies masu kula da Aman da Amali, sai biyu masu gyaran gida da aiki, Nanies din su Aman inason yan Philippines dinnan irin yan shekaru 40 educated ones dazasu din tayasu yin homework, sai I want a chef mai girki yar tsohuwa hakanan sai mai shara da gyaran gida kuma yarinya age 12-15 haka kada tawuce 15yrs, I don’t care konawane salary su i will pay” dasauri Zeenah tace “lemme call my personal person goben nan zakiga tasamo miki” tace “kira nima I will call my lawyer I just have to sue Nura let’s settle this score, koda zanyi withdrawing lawsuit din daga baya but yagadai i can take action idan yataba lafiyan jikina sabida karya kara kuskure yace zai taba educated independent woman like me” ihuu Zeenah tayi tahau tafi tace “now you are talking, my friend is back kicima Nura kutumar babakeren uba, ke maza fa sunfi tsoron maicin ubansu” dasauri Hadiza tace “I believe you ai sanyin danayi kwana biyu yasa raini ya gitta tsakaninmu wai harda marina, ni Nura zai daga hannu ya mara, kinga snap my face i will use it as evidence” tabama Zeenah wayanta, karba Zeenah tayi tadauki hotunan fuskan Hadiza harda cemata “yi kaman wacce taci kuka takoshi” Hadiza tai haka tai clicking snap tabama Hadiza wayan, duba hotunan tayi ranta na kara baci sabida yanda yatsu biyar suka fito a fuskanta dodar dan da duka karfinshi na maza yamata marin saida taga duhu. Mikewa tayi tace “kutashi muje lemme go nayi gyaran jiki and facials kafin hannunshi yazama permanent tabo a fuskana. Tashi sukayi sai kawai ta rungume Zeenah tace “I love you best friend, you are better than my own blood sister, you just brought back light into my life” Zeenah tace “absolutely no man aduniyan nan ya isa yace zai takamu wlh, we know our right, mari fa ko a shari’a batada kyau, ai Nura deserves more, ki yarda wani stupid love who love help kuyi settling score yakoma yana tsoronki zakiga wlh zai shiga taitayinshi” Hadiza na murmushi tace “da ina cin ubanshi ma yafi sona, yanzu dana dena wai Nura ne yasamu liver daga hannu ya kodamin mari ni Hadiza, I will mess him up wlh”. Suka wuce suka fita daga gidan. Jama’a like I said I just wanna portray the major issues dake kawo rabuwan aure a zamanin nan sabida ku gani kusan daga ina mistakes din ke zuwa, ta yanda zamu karanta mu gyara idan munayi dan believe me most of us munada one of two dabi’un Hadiza Allah dai ya kyauta yakuma shiryan damu. But then I have a question, what do you think can change mata masu strong opinion din Feminism??? Note dukan mace baida kyau fa, please maza masuyi su dena, cus kahadu da macen datasan kanta she can ruin you completely da career ka so adena dukan 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣5️⃣ *ROYAL JELLY* *(MAIDA TSOHUWA YARINYA)* 🔥🔥🔥💃💃💃💃 Wani kayan sai amale wannan supplement shi akecema maida tsohuwa yarinya ita Kuma yarinya ta koma jaririya😂💃💃💃💃💃💃💃💃💃 Ina kuke Mata masu aji waanda sukeso suga suna walwali kamar tauraro toh gafa dama tasamu kiyi washar washar abinki.....🔥🔥🔥🔥⭐⭐⭐⭐ ⭐👑 Royal jelly nasa jikin mace yayi glowing mace jikinta yayi Kamar tangaram😍😍 ⭐👑 Royal jelly natsoro da gashin mace yayi kyau ⭐👑 Royal jelly na gyara mace ciki da wajenta ⭐👑royal jelly na fidda shape din mace...💃💃 ⭐👑 Royal jelly na Hana fatar mace tamukewa , yasa tayi looking fresh ⭐👑 Yanasa mace yayi looking under age dinta💃💃💃💃💃kiji ana wacce ke kullun kamar wata budurwa🔥🔥🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly nakara hasken Ido yakuma gyara gashin ido 🔥🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly na tsirar da farce da kwarinshi... Idan kinji ana maganar glowing to kici birki a royal jelly 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥⭐⭐⭐👑💃💃💃 https://chat.whatsapp.com/KU8Mqd2Mo530Pc14hc7QOG 25 Waiwaye baya kadan. Yau kwanan Ummi uku agidan kanin mijin Ya Aisha dashi da matarshi basu da matsala matarshi saita zama mata nabiyu da Ummi tayi kawance a duniya, itadai Ummi binsu take bazata iya kirga wajajen da aka kaita ba tayi thumb print, anmata passport menene menene. Dukta rame sabida yanda tunanin Nura ya addabi zuciyanta kusan bata iya baccin dare most time da safe bayan asuba take bacci. Yauma kaman kullum tana zaune matar gidan ta shigo da waya a hannunta tace “gashi Ya Aisha ce” amsan wayan Ummi tayi matar tawuce tafita ahankali tace “Hello Ya Aisha ina wuni” murmushi tayi tace “Ummi ya kike hope yau kin tashi lpy, baki kuka jiyaba ko” dan murmushi Ummi tayi tace “banyiba” shiru Anty Aisha tayi chan tace “Ummi Hajiya nacikin damuwa sosai sabida ke ciwonta na neman yatashi, tace nasa akaiki kano immediately” dan bugawa kadan zuciyan Ummi yayi dan wani kalan kunyan Hajiya taji tanaji Ya Aisha tace “nasa Ahmad yamiki booking flight jirginki is by 1, kije wajen Hajiya Ummi tace bata yarda kizo Egypt wajena ba, nayi nayi nayi da ita taki, namayi magana da Gwaggo yanzu kafin kafin nakiraki ta yarda kije Kanon tunda Hajiya takoma kano” cikin sanyin murya Ummi tace “Hajiya nada ganin likita a Abuja mesa takoma kano”? Dan murmushi Ya Aisha tayi ganin even cikin damuwa Ummi still cares about Hajiya tace “sabida ke mana antaba mata diya” hawaye Ummi taji sun zubomata tace “Ya Aisha nama mamana laifi nasan tana fushi dani taya tana gari zan kama nabar gida batare dana jirata ba” Dan murmushi Ya Aisha tayi tace “kada ki damu Hajiya bata iya fushi damu yaranta ba, zata yafemiki, yanzu tashi ki shirya, idan kikakai kikai settling zan kara magana da Hajiya nafiso kizo nan kiyi karatu abinki, yau koda baki tareda Nura this is the least abu dazan miki Ummi kinfi haka wajenmu” Gyadamata kai Ummi tayi sukai sallama. Wanka Ummi tayi ta shirya Matar Ahmad tamata kyautan sabon atampa da takalmi suka kaita airport sai kano ita Ummi abin har mamaki yake bata yanda itane tane hawa jirgi haka tana sauka ga mamakinta taga Meena da gudu Meena ta rungumeta saikuma ta kama hannunta har zuwa wajen wata babban jeep da direba ke gaba yana jiransu suka shiga sai gida, wowww gaskiya Nura naji da Mamanshi babban hadadden gıda ya ginamata durmemen gaske fa ga motoci biyu, da jeep dawata karaman Camry, ga masu taya Hajiya aiki dan indai tana gari tana bada abincin sadaka duk ranan duniya da magrib haka almajirai da yara zasuyi layi akofar gıda. Suna shiga babban falon gidan Hajiya suka gani zaune kan babban lallausan carpet nata rikeda charbi a hannu hada ido sukayi da Ummi data sauke idanunta kasa da sauri ta tsugunna ahankali tace “Hajiya ina yini” ba yabo ba fallasa tace “sannu da zuwa Ummi” takalli Meena tace “kaita dakinta ki kawo mata abinci taci tahuta” Meena takalli Ummi da kanta ke kasa tace “tashi muje ciki Ummi” kasa tashi Ummi tayi Hajiya tace “tashi kuje ciki Ummi” da kyar Ummi ta iya tashi tabi Meena sukaje ciki wani lafiyayyen dakine aka kaita ahankali Ummi da idanunta sukai ja tace “Meena Hajiya fushi take dani” hannunta Meena takai ta share saman idanunta tace “bake kadaiba, harda ni, da Ya Nura, da Ya Aisha ma data boyeki bata tashi gayama Hajiyaba sai jiya, nihar tausayi tama bani da Hajiya ke surfafa mata, amman yanzu tunda kinzo nan matsala yazo karshe damuwanki yasa taketa fada, kibar Hajiya da Ya Nura itane daidai shi kuma kada ki damu Hajiya batada riko zata sauko, jeki alwala bari na kawo miki abinci” gyadamata kai Ummi tayi tawuce tafita tazauna tai shiru Meena ita ke keeping nata company Hajiya baruwanta dasu. Wuraren 10 Ummi ita kadai adaki dan dakin Meena daban dudda taso tazo ta kwana da Ummi Hajiya ta hanata Ummi taji takasa bacci, Hijabi ta dauka tasaka tabude kofa tafito, dakin da Meena ta gwadamata dazu shine na Hajiya tawuce tadade gaban dakin kafin tayi sallama ahankali tareda budo kofan kadan Hajiya na zaune tasa wani farin glasses a idanu da wata yar littafin azkar a hannunta takalli Ummi tareda yin shiru batace komiba, ahankali Ummi tashigo dakin tareda maida kofan tarufe tazo har gaban gadon sai kawai tayi kneeling taredakai hannayenta takama kunnenta tabude baki zatai magana saikuma takasa tafashe da kuka sosan gaske yanda kasan Mama da yarinyanta datai babban laifi tace “Hajiya wlh nasan namiki laifi nafi kowa sanin haka, na tafka shirme nayi kuskure banyi tunanin abinda ya chanchanta daniba, dan Allah Mamana kiyakuri ki yafemin wlh fushin ki na cimini zuciya sosai” tafashe da kuka sosai fa kaman ana dukanta, Hajiya shiru tayi tana kallon Ummi sosai kukanta ya tsuma zuciyanta bana wasaba, da ace wani zai shigo dakin nan zau dauka ita ta haifi Ummi sabida yanda yarinyar tabata girma tana kuka iya kuka agabanta, zamanin nan da wuya kasami suruka dazatazo tana kuka tasa guiwa akasa tana rokonka gafara kan laifin dabai taka kara ya karyaba, Alhamdulilah yau tana kara godewa Allah daya kawo Ummi rayuwan Nura, cus yarinya ce ta arziki, ga kunya ga ladabi ga biyayya, banda haka Ummi ta daraja ta tadauketa matsayin uwa, ahankali ya ijiye littafin hannunta tareda nunama Ummi gefenta tace “zoki zauna anan” kasa tashi Ummi tayi tana girgiza kai, kayattaccen murmushi Hajiya tayi tace “Ummi komi yawuce amman nan gaba kada ki kara abinda kikayi, shi aure hakuri ne Ummi, dole yau kaga daidai gobe kaga ba daidaiba, maza mazane! Abinda ya batamin shine ina gidan, ina garin baki tunanin ki jirani ba ki sanar dani kika kama hanya kikai tafiyan ki, Aisha ta sanar dani komi nace sam ban yarda ba, ke matar aure ce Ummi bai dace ta daukeki ta tsallakar dake gabaki daya daga Nigeria zuwa wata kasar batare da sanın mijinki ba ai Nura yasan abinda tayi bazai taba yafemata ba gwara koma menene kina gidana ni mahaifiyarsa” Hajiya tadanyi shiru tace “Nura bai kyautaba I support tafiyanki sabida inaso shi da kanshi ya gane amfaninki ya gane ko yana sonki koba yayi, Nura dana ne amman bazan yarda ya cuci kowace yarinya aduniyan nan ba, idan bai nemeki bazan taba cemai gakiba, amman kisani indai kinyi aure dole ki kulla dammaran zaman aure, aure ba abin wasa bane Ummi kina jina”? Gyadamata kai Ummi tayi, Hajiya tace “mujira gudun ruwanshi, gidanan nan naki ne kome kikeso kiyi, zan sakaki awani islamiyya na matan aure da akeyi karfe goma zuwa sha biyu kullum banda asabar da lahadi, asabar da lahadi akwai wani school haka danakeso ki shiga English school ne zaki shiga Meena ma tashiga dudda ta gama school, amman banda magana da maza ke matar wani ce kina jina” gyadamata kai Ummi tayi, Hajiya tace “idan Nuran yazo zanyi magana dashi idan zamanki kano shiyafi ma kiyi zamanki anan dudda ba lallai ya yarda ba dan shi mutum me da yanaso iyalinshi aduk inda yake amman zanyi idan ya yarda yanada gidanshi anan kiyi zaman ki, sannan kiyakuri da komi daya faru kinji” gyadamai Hajiya kai tayi sunyi magana sosai Hajiya sai bata shawarori take tana advising nata har wajen shabiyun dare sannan tasata taje ta kwanta. ** After 1 nadare Nura yadawo gidan dakin Aman yawuce yayi kwanciyan shi, 4:30 yatashi as usual sai kawai yawuce dakin Ummi wanka yayi awajen yabude wardrobe yanada wasu kaya awajen ya shirya tsaf dan baiso yadawo gidan idan yafita asuba kawai yawuce yafita masallaci yaje 6 yadawo yashiga mota yabar gidan, office yatafi yazauna yayi shiruu zai iya cewa tunda yake aduniya baitabajin kalan kuncin nan da rashin farincikin nan dayakeji ba, lumshe idanu yayi yatashi daga kujeran sai kawai yazo tsakiyan office din yasami dogon kujera yazauna ahankali ya lumshe idanu kusan awa biyu yana ahaka kuma ba bacci yakeba, knocking akayi tareda bude kofanshi aka shigo Alhaji Musa ne yana sanye da manyan kaya hade fuska tamau Nura yayi ya yunkura yatashi da sauri ya dan dafe kanshi dayaji ya saramai da sauri Alhaji Musa yazo wajen yace “Nura lafiyan ka kalau bakada lafiya n……” hannu Nura yadaga mai yakalleshi da jajayen idanunshi yace “mekazo yi a office dina”? Bin Nuran yayi da kallo saikuma ya zauna kan center table yace “kai dalla chan maganan danayi ranan ne har yanzu azuciyanka I just did that danka gane kanason Ummi ne” kallonshi Nura yayi Alhaji Musa yace “wlh da gaske, listen abokina koda ace lokacin daka auri Ummi you were not sure kana sonta ko baka sonta believe me idan nagaya maka yanzu kanayi, kai kaga yanda ka chakumo ni ne Nura saida na firgice yanda kasan dan gidan dambe kaman wani wrestler, na shaku fa a hannunka wuyana har yau ciwo yake saida naje Likita ya dubani” dan murmushi kadan Nura yayi baice komiba, Alhaji Musa yace “Nura kaga you are too soft ne, kadena bari mata na chaza maka kai abanza awofi, kaifa namiji ne kaine me mulki, yau ko mata biyu kakeso ka karo atare zaka iya, da karfinka da kudinka ai wlh sai inda mai yakare so common chill, amman dai kaje ka dauko Ummi yaci ace by now ka kira Kakanta, kadaina nuna musu taurin kai hakan rainine Nura, am sure inda Hadiza ne da yanzu ka kira gida ko kamaje dan kaga Ummi ne is that why kake abinda kakeyi”? Girgizamai kai Nura yayi yace “Ummi hurt me deeply Musa, even Hadiza dake abun mahaukata bata tabamin abinda Ummi tayiba, ban taba having issue ta kama tabar gidana ba, Hadiza belive in fighting her battle da kanta bata gudu ba, she’s not a coward” Alhaji Musa yace “yo ai yarintar kenan, Hadiza ta girmi Ummi, banda haka Ummi batai karatun da Hadiza tayiba yarinyar is not expose, a kauye fa aka haifeta ta girma, the poor thing must’ve felt bata da kowa she’s alone, bakada time nata, baka dauki wayanta ba tazo kuma kamata koran kare without speaking to her ko kallonta, gaskiya Nura baka kyautaba yaushe zamuje mu daukota” dan ijiyan zuciya Nura yasauke yace “tunda gobe Alhamis mubari asabar” Alhaji Musa zaiyi magana akai knocking kofanshi Nura yace “come in” secretary Nura ne tashigo dawani sealed file haka a hannunta tace “sa yanzun nan wani yakawo maka wannan daga Attorney’s Chamber na Maitama” Alhaji Musa yace “Kanada wani court case ne, ina lawyer ka maiya hadaka da yan Attorney’s Chamber nan bayan kasan barayi ne” karban file din Nura yayi looking confuse yace “ni I don’t have any business awajen kodai mistake akayi”? Saikuma yaga sunanshi full name nashi agaban file din yace “ba mistake bane ga sunana” yakalli secretary yace “you can go” tawuce tafita Nura yashiga bude file din, yaciro takardun ciki yashiga karantawa kaman wanda akacema yayi freeze kawai yayi freezing dasauri Alhaji Musa yace “lafiya menene?” Dasauri ya karbi file din gabaki daya daga hannun Nura yana karantawa dasauri yakalli Nura yace “ana nemanka gobe by 10:AM nasafe a kotu, Hadiza tayi suing you for domestic abuse!!” Sosai Alhaji Musa ke kallon Nura dayayi mutuwan zaune ranshi abace yace “meya faru kuma I thought kacemin kun shirya kun maida komi past, why is she suing you for domestic violence? Kasan hakan zai iya sa kaje prison for good 3yrs kuwa? Is Hadiza trying to ruin you and your career or what, meka mata?” Sai alokacin yasaki dan murmushi da zai nuna maka how hurt he’s deeply yakalli Alhaji Musa yace “I slapped her jiya!” Cikin tsananin fushi Alhaji Musa yace “wlh there’s nothing you can tell me Nura mata yar boko batayi bane aduniya sam sam! Allah ya wadaran matan I know my right, I know my right, kai!” Musa yayi ihu ranshi yayi matukar baci danko ba’a gayamai ba yasan waye Nura ba mutum mai dukan mata bane koda ya mari Hadiza jiya shi yasan wlh ba karamin abu bane zaisa Nura yadaga hannu ya Mari Hadiza ba. Ganin yanda Nura yayi shiru yakasa motsin kirkima saiyaji yabashi tausayi, look at Hadizan daya wulakanta Ummi sabida ita thinking ta chanza yanzu zasu more rayuwa su dawo lovers din dasuke ada, dudda yaki admitting wulakanci yama Ummi but just look at abubuwan da Hadiza keyi, meke damun matan zamanin nan ne? Ta ina namiji da mace suka taba zama daya iyye? Wai what is wrong with matan yanzu ne haka iyayensu sukayi? Ba’a musu tarbiya bane agida? Iyayenmu mutane masu daraja mazajensu ne, kusan bauta musu ma suke, basu ganin yanda iyayen su ke rayuwa da mazajensu? ilimi haukane? What is keda mijinki dayane, ke kawai abarki kiyi komi yanda kikaga dama? Miji yace A, kice B har zuwa Z, ace kiyi kice bazakiyi ba, mesa wasu matan keda brain din fish?? Zama yayi kısada Nura ahankali yace “idan kaje goben just buy lawyer nata kawai akashe case awajen kafin alkali yazo, da kudinka a aljihu karka wahala abanza” murmushi Nura kawai yayi ahankali yama kasa cewa komi sai chan yace “Musa bani labari dan Allah” Musa jiyayi idanunshi sun cicciko da hawaye Nura yabashi tausayi ana wani zamani da kullum mata ake tausayama cus mata are weak waye, waye, waye but wlh idan akai looking deep akwai wasu matan da kawai sunfi karfin mazajensu ne duk ta yanda zaka kalli abin, infact matan ke soyama mazansu aya a hannu not the other way round, Hadiza na yanda taga dama da Nura kodan taganshi mutum mai hakuri ga yafiya sannan yana sonta, Nura is this type of person that hates hurting mutum baida riko that is just Nura, jibi dai abinda yamai jiya na ya saki Ummi ya aura da wanine yau bazai kulashi ba but because Nura is just Nura magana daya biyu sun shirya kuma har abada ya manta da maganan kenan, that is just Nura is his personality his nature bazaka iya chanza wa ba, ai shi kanshi wani zubin yakanji haushin Nuran for yanda yake barin Hadiza na getting away da so many things, haka kawai Allah ya yo shi, Nura hates hurting mutum, Nura nada hakuri, Nura nada yafiya, sannan Nura ya tsani takurama mutum inhar u are happy da abu zai barki kiyi, da ace zai iya zuga Nura dudda ba’a shiga tsakanin miji da mata dan just imagine abinda yama Ummi balle ma shi Aboki daya zugashi ya hakura da auren Hadiza kawai gabaki daya, taje ta auri namiji da baida matsala da mata maiyin feminism shikenan. Amman banda jakanci da bahaggon tunani irin na Hadiza mutumin da yau shekara nawa kuna aure bai taba dukanki ba yau saiki makashi a kotu yana uban yaranki bazaku iya resolving issue din agidaba saikin tonamai asiri a duniya, and jahilcin da mata keyi is saisu dinga maka abi suga kaman kai sukema not knowing anything dazaiyi affecting Nura is affecting her as well koda ba directly ba, duk abinda yayi affecting Nura ayau will affect yaranta koda ace ma basa tare, if something affects yaranta ai yayi affecting nata as well so then menene riban tonama kanku asiri aduniya?? Sabida mijinki ya mareki sau daya in 10yrs kına tonama kanku da yaranku asiri wlh Hadiza is so shameless bamata da kunyan duniya. Dafa Nura yayi ganin baison maganan yace “kasan Maman Humaira tasoma sakan mini gurasa fa dana nunata ke kinga nabi Alhaji Nura kauye yakaro aure nima fa auren nan nakeso nayi shine ta natsu” Sosai Alhaji Musa yadinga ma Nura hira, office dinshi dabaije ba kenan har 1 nadare wlh suna tare just because baiso yanarshi shi kadai cikeda damuwa sannan suka koma gida. Yauma adakin Aman ya kwana 4:30AM yatashi yayi wanka yasa kaya yabar gidan zuwa masallaci around 6 yadawo gidan zai bude mota ya shiga aka bude kofan falo Hadiza ne tafito tana sanye da bubu yana kokarin shiga mota tace “wato kaga sammaci bazama kazo ka rokeni, be on your feet and genuinely bag sabida nai withdraw the case ba” kallonta Nura yake daga head zuwa toe sai kawai ya shiga mota bai cemata uppan ba, abin ya masifar kular da Hadiza kaman ta kurma ihu wato ita zai maida mahaukaciya dasauri tazo wajen yana kokarin tada motan ta tsaya wajen kofan tabude cikeda rashin kunya dan yanda kasan zata makeshi tace “ohhh ni kakema girman kai imagine level na ignorance naka, don’t worry zakayi ladabi a prison yau stupid wicked man kawai mayaudari kawai” hannunshi yasa yakalleta yace “saki”ihu tamai da saida gateman yafito da gudu tace “bazan saki ba Nura!” Kallonta Nura yake idanunshi har sun kada sunyi ja, Hadiza tace “zanyi maganinka Nura, wlh zanyi maganinka dan kai karamin da duniya ne, muhadu by 10” tawani bugamai kofan motan Allah yasa hannunshi baya wajen da wlh saiyay sustaining injury jan motan Nura yayi batare yabar gidan, Hadiza jitayi ranta na baci har kasan zuciyanta bata wani so suje court dinba taso yazo ya lallasheta kawai ta kira ta janye case din saisama ganin bai biyota ba ita tazo nan tunda ta tashi take gadinshi yadawo daga mosque a window ta falo, tana ganin yadawo tafito with hope zaiyi sulhu da ita, koyadan mata magana mai kyau amman jibi yanda yamata banza ya mai data mahaukaciya sai taji gwarama data makashi kotun, juyawa tayi takoma ciki. Karfe goma daidai motan Nura yayi parking gaban kotu inda Alhaji Musa ke tuki already Lawyer Nura na kotun, fitowa sukayi jiki asanyaye suka wuce ciki gaban court room din yaga lawyer shi tsaye yana ganinsu yace “yauwa muje ciki yanzu Alkali zai shigo”. Ance a woman can make or break a man kun yarda??? Hadiza made this statement kana ganin karo aure shine zai baka peace din dakake nema to bazaka taba samun peace din nan ba, from abinda muke gani Nura ko yakasa samin peace din dayake craving right??? What action kuje ganin yakamata Nura yadauka akan Hadiza?? Yakokarin ya gyarata ta baki taki, yayi ta love taki, yayi ta family taki, Mezaima Hadiza ta gyaru???? But then again NURA yabani tausayi is not easy wacce ka keso tai hurting naka😭 Hadiza fans I have just one question danake so namuku, inhar Love bai chanza Hadiza ba, me kuke ganin zai iya cire wannan feminism din daga jininta??? Mata maza 🔊 Dukan mace ke jawo case din dambe between mata da miji, daganan kaga an kashe juna, ko mata ta kashe miji ko miji ya kashe mata, ko ajima juna rauni mai muni Allah ubangiji ya shirya damu. 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣6️⃣ https://chat.whatsapp.com/KO6bdcXjxmh2l6pM6T0meI In mutum yanason yayi register Kuma yayi siyayyar 🌟3 free registration ne Kuma Ina adashen products din GHT in mutum beda halin Siya Nan take 08066136431 Note: Ni ba lawyer bace! Though I consulted some lawyers irin su Majal and co😍 Incase kunga mistakes no mind me, I be health personnel ejor❤️ 26 Shiga cikin court room din sukayi hada ido yayi da Hadiza dataci gayu yanda kasan zataje gasan kyau tana sanye dawani vilisco embellish atampa maroon ta kafa daure tayi kyau gefenta kuma Zeenah ne zaune itama ta kallo Nuran, dauke kai yayi daga kallonta yawuce yazauna kusa da lawyer shi while Alhaji Musa yazauna a daya daga cikin kujeran dake row din bayansu, Hadiza itama tashi tayi tawuce tazauna kusa da lawyer ta wata attajiran mata ne haka taci glass Mrs Oyenyi Chichi Ebenezar, daidai nan Alkali ya shigo aka tashi akai introducing case din sannan aka kira Nura kanta yafito ya tsaya yayi rantsuwa Mrs Oyenyi ta mike taje gaban Nura ta tsaya tace “Mr Nura kaida Hadiza has been married for 10yrs 9month correct?” Anatse Nura yace “yes” anatse matan tace “describe relationship dinta dakai a tsawon shekarun” dan shiru Nura yayi saikuma ya kalli Hadiza dake kallonshi kyur, Mrs Oyenyi tajuya takalli abinda yake kallo tace “are you trying to blackmail my client Nura”? Dauke idanunshi yayi yace “no” Mrs Oyenyi tace “to bama kotu amsan tambayan da na maka” ahankali Nura yace “relationship dina da ita is just like relationship din any other couples, we live, we share good moments and we have arguments just like every other couples do” Mrs Oyenyi tace “babu any history of abuse ko molestation” Dasauri Lawyer Nura yace “objection my lord, mesa take sa magana abakin client dina is just kaman tariga tai concluding cewa client dina is an abuser” Alkali yace “objection overrule cigaba” Mrs Oyenyi tai murmushi tana kallon Nura tace “ina jinka Nura” Dan shiru Nura yayi sai chan yace “bantaba molesting Hadiza ba or abuse her banda ji…….” Mrs Oyenyi tai blocking nashi tace “matanka tace kasha molesting nata not once or twice ko bataso tai wani abu dakai kanayi” dafe kanshi Alhaji Musa yayi cikeda rashin jin dadi, dasauri Hadiza ta waiga ta kalli Zeenah cikin whispering tace “bancema Mrs Oyenyi yana molesting dina ba what is she saying?” Cikin whispering Zeenah tace “ni nace takara dashi sabida yaji ajikinsa ai kin gayamin abinda yamiki kenan daya auro Ummi” cikeda rashin jin dadi Hadiza zatai magana Alkali yace “silent” akai shiru, Mrs Oyenyi tajuya tadawo gaban bencinta tadauki wani file ta taho ta bayar tace “mai girma mai shari’a Nura yasha yima client dina fin karfi, ihu, harma yakai yana dukanta yanzu, cikin file din nan na dauke da evidence na farko hoton fuskan Cleint dina ne Hadiza da fuskanta dazaka ga yatsu biyar na Nura sunyi jazur a fuskanta wanda har yakaita ga asibiti aka dubata takarbi pain killers, sannan auren Nura yazama babban damuwa ga client dina bata da kwanciyan hankali da peace of mind agidanshi haryakai ga just about a weeek ago tana asibiti for case na heart sabida damuwan shi duk evidence na medical history nata is there, ina mai rokon kotu ta bima Hadiza hakkinta duba da irin fighting datayı for her life a hospital for the past two weeks duka duka yaushe akai discharging nata amman harya mata kalan wannan marin what if marin yayi leading nata takara samin cardiac arrest bayan yasan clearly an fadi a asibiti bazata kara surviving ba??” Tashi lawyer Nura yayi zaiyi magana da sauri Nura yadagamai hannu alamun baiso yayi magana yazo dashi nan ne dan kawai yamai arranging bail da sauran formalities, ahankali Nura ya kalli Alkalin dake kallonshi ganin yahana lawyer magana yace “Yallabai I am guilty!” Dasauri daga Lawyer shi har Alhaji Musa har ita Hadizan suka kalli Nura dan bata taba tunanin Nura ko lawyer shi bazasuyi gardama ba, dan shiru Nura yayi chan yace “I let my emotions get the best of me, and I sincerely apologize for that” ahankali yadaga kanshi yakalli Hadiza yace “Hadiza am sorry for slapping you and for all d pains dakikace nai causing miki” Nura zai magana Lawyer shi yatashi da sauri yace “Mai girma mai shari’a client dina ya yarda yayi laifi kuma yabada hakuri muna pleading for mercy to pay fine na domestic violence din da duka charges dinma” dan hamdala Hadiza tayi tana karkada cinyoyinta dan feets nata are so cold batason akai Nuran ta gidan yari she’s just hoping ayarda ya biya fine din. Tass Alkali yagama rubuce rubucen shi kafin yadago yace “kotu ta yaba da yanda Nura bai bawa kotu wahala ba, ya karbi laifin shi sannan yabada hakuri, duba da baida wani bad record kotu ta yanke hukuncin rike Nura harsai yabiya fine na naira dubu dari uku, 300,000!” Dasauri Alhaji Musa yace “Alhamdulillah” Alkali yace “idan akwai wanda keda wani magana cikin parties din zasu iyayi” hannu Nura yadaga hakan yasa Alkali yace “ina jinka” tashi Nura yayi ya kalli Alkali anatse yace “inason kotu ta shaida ni Nura na saki matata Hadiza SAKI DAYA!” Wani kalan dum! Dummmm! Hadiza taji azuciyanta yayi dawani kalan sauri tadaga kanta takalli Nura hannunta na rawa rawa, Nura na kallon Alkali yace “inason kotun nan tazama shamaki tsakanina da ita, kada Hadiza tasake daga kafa ta taka gidana! Duka wani abu nata na cikin gidana daidai da cokali zan tattara nasa a mota yau ba gobe ba na aika gidan iyayenta inda na aurota, sannan kada ta daukan mini yarana! Alkali inaso kamin katanga da ita!” Hawaye Hadiza taji zasu zubo daga idanunta tarikesu gam tana fuzgar da iska da baki kirjinta kaman ana barza masara dasauri Zeenah tazo ta bayanta tana mata whispering “kada ki kuskura ki nuna kinji wani abu dan dadi zaiji, abinda yakeso yagani kenan” daurewa Hadiza tayi ta rike hawayen Alkali yagama rubuce rubuce yace “you can sit” yakalli Hadiza yace “kaman yanda kikaji mijinki ya sakeki kuma yamiki shamaki da gida wanda yake nashi, dan haka kada ki kara sa kafa agidan shi kikai haka zai iya daukaka kara akanki, zancen yara kuma dake da shi zaku iya daukaka kara kuyi case na custody yara” cikeda karfin hali Hadiza tace “no need yara nawa ne ko suna hannunshi ko suna hannun uban idan inason ganinsu zan kirashi shiya kawominsu, kuma dama koda bai sakeni ba ni zancemai ya sakeni, me akeyi da namiji mai dukan mata” wani dadi Zeenah taji hardama Hadiza tafi kasa kasa Alkali yace “kotu tazo karshe” yatashi yafice police sukazo aka wuce da Nura lawyer shi da Alhaji Musa suka bisu, court room din yarage saura su Hadiza, hawayen da Hadiza ke rikewa ne suka zubomata wlh bazamata iya describing in words how she’s feeling right now ba, bata taba expecting Nura zai saketa ba sabida ta makashi a kotu, tunanin baimazo ranta ba yanzu Nura yamata saki biyu kenan, Mrs Oyenyi da bata wani san komiba ita she’s just a lawyer tace “why are you crying? You should be happy a man like this dayayi inflicting so much pain in you yasake ki infact this calls for celebration ma” Zeenah tace “owooo tell her oo Mrs Oyenyi, I don’t know why Hadiza base her whole life on this guy not knowing yanzu ne zaki fara cin rayuwanki da kyau dakuma tsinke, ni dayama miki biyu yacikashe” dasauri Hadiza tadago jajayen idanunta takalleta Zeenah tace “yes you should be free of this Nura for good haba yanzu kuma abin takaici kina wani zubar da precious hawayenki sabida namiji wlh tir Hadiza kinji kunya, you are a disgrace to mata damukasan ciwon kanmu, you are a disgrace to all feminist out there” hannu Hadiza tasa ta share fuskanta tass tai murmushi tace “ba ina kuka sabida Nura yasakeni bane Zeenah, kuka nayi sabida kalman saki feels somehow ajikin mata, but danya sakeni sai mene harda wani amini katanga da gidanshi tunda gidan dirhami gareshi ko gidan sarkin dubai ne dashi ko prince of Saudi useless Man gidan da I can buy like 10 of it” Zeenah tace “owooo, tashi mutafi jor let’s go and celebrate book hotel and sleep today kafin gobe muje house hunting” dasauri Hadiza tace “gidan ki fa? I thought anan zan kwana”? Dan murmushin yake Zeenah tayi tace “ohh my bad ni nama manta ba matsala saiki kwana agidana, muje let’s call Baraka and pick her up a hanya” tashi Mrs Oyenyi tayi sukai sallama daman sun gama biyanta suka wuce ahanya suka dauki Baraka wacce Sam bataji dadin labarin ba amman ina ruwanta, deep down Hadiza is so worried amman Zeenah taki bata room to show how worried she is kuma itama din batason suce tacika depending on a man ko she’s a disgrace to feminist. Sai bayan magrib suka tafi gidan Zeenah, babban gidane mai kyau but baimakai gidan Hadiza girma da kyau dinba dudda matar minister ce, shiga sukayi ciki, Zeenah na murmushi tace “ai you are full ko kina bukatan abinci naga munci mun koshi a inda mukaje bari nabaki ruwa kinsan ni yan aiki na basa kwana da yamma suke tafiya saisa kikaga zan baki ruwa da kaina” Gyadamata kai Hadiza tayi Zeenah tadauko ruwa taba Hadiza tace “muje na kaiki dakinki” dan kallonta Hadiza tayi saitaga kaman she’s rushing ko ruwan fa bata budeba amman bata damuba ta tashi tabita sukaje sama takaita wani daki tace “to saida safe”gyadamata kai Hadiza tayi dudda she wanted su danyi hira har zuwa irin 12 din nan nadare but she guess tagaji tunda tun safe suna tare wucewa Zeena tayi agurguje ta sauko kasa ta kwashi takalmin Hadiza dake gaban kofa tashigo dasu da sauri ta wuce kitchen dinta taboye takalmin abaya shi kofa sannan tashiga kitchen agurguje fa tashiga hada girki. Hadiza datagaji dan bayan tayi sallan isha’i bacci yayi awon gaba da ita cikin bacci mai nauyin gaske taji hayaniya da kaman karan fashewan abu hakan yasa ta bude idanunta ahankali baccin na fita daga idanunta muryan namiji taji yana cewa “takalmin waye wannan Zeenatu? Wakika kawo gidan nan bayan nagaya miki banason ana zuwa mini gidana?” muryan Zeenah taji kasa kasa bataji metake cewaba saikuma chan takarajin karan fashewa abu kaman plate haka ko glass cup yayi ihu yace “ubanwa yace ki kawo mini wata kawarki gidana I don’t care if she’s squatting here sabida mijinta yasaketa, are you deaf? Are you stupid, gidan ki ne? Is this house yours? Who do you think you are Zeenatu dazaki dinga shigo da mutane ba tareda kin sanar da ni ba? Oya go and call her ta tattara yinata yinata tabarmin gidana inba hakaba wlh kema koranki zanyi yanzun nan” zaro idanu Hadiza tayi saikuma ta dafa kirjinta Zeenah ne da mijinta ke fada haka akanta ake magana ko wata kawan daban? Tashi tayi ahankali tabude kofan dakinta tafito tayi tafiya tadan leka downstairs ta yanda basa ganinta Zeenah tagani tayi kneeling awajen dinning da duk an faffasa plates tahada hannunta biyu harda kuka tana rokon wani attajirin mutum dabai wani tsufa ba kaman Nurin ta yake, murya kasa kasa tana cewa “dan Allah karufamin asiri kada ka tozar ta ni kabarta ta kwana gobe zata tafi i promise” kana ganinshi kaga masifaffe har zufa ke keto mai a hanci da goshi, ga takalman ta dataga an wawwatsar a falo mutuwan tsaye Hadiza tayi dataga yadauki cup yakara bugawa a katsa ita kanta Hadizan saida ta firgita kaman glass zaizo nan sama inda take ya shiga jikinta cikin fushi yace “stop begging me useless woman who are you dazaki dingayi yanda kikaga dama agidana, jeki kira kawar naki kubar gidana dagake har ita” hannu Hadiza tasa ta taushe bakinta mamaki sai kawai ta juya fuuu cikeda zuciya dan tafi karfin wulakanci akan wannan kurkukun gidan tawuce dakin datake tadauki handbag nata kawai tashiga saukowa jin tafiya yasa dukansu suka juyo dasauri Zeenah ta mike tana goge fuskanta ta kakalo murmushi cike da duniyanci tace “Hadiza zoki gaisa da Baby hala karan plate ya tadaki daga bacci ko dan dazu na leko naga kinyi bacci, wlh bari mukayi yanzun nan” wani kallo Hadiza kema Zeenah yanda tayi just now kaman hawainiya sai kawai ta tsinke da lamarinta batace komiba tace “ina key motata”? Center table Zeenah ta nuna mata Hadiza na tsallake tsallake kwallaben dakenan har falon tawuce tadauki key motanta ta kwashi takalmanta tai wajen kofa cikeda zuciya Mijin Zeenah ya nuna Hadiza da hannu yace “jibi mara kunyan da kike cewa ta kwana agidana taganni bata iya gaidani ba” azuciye Hadiza ta juyo tace “anki agaidakan mata mutuncin mahaukac…….” “Hadizaaaaaaa!!!!!!” Zeenah tama Hadiza wani kalan ihu kaman zata tsaga gidan tace “karki kuskura ki zagin mijina wallahi cus zakiga other side of me” baki Hadiza tabude completely flabbergasted tana kallon Zeenah, saikuma chan ta nuna kanta tace “Zeenah you, me!” For the first time in history the chatterbox Hadiza was speechless tama kasa constructing sentence tsabagen shock tana kallon camellion Zeenah, Zeenah tace “yes zaki shigo har gidana ki zagi mijina are you okay an gayamiki irin ex mijinki ne shi Nura”? Shiru Hadiza tayi tana kallon Zeenah, zata sake maganan mijin Zeenah yace “kneel down ki gayamin wace jakace wannan mara tarbiya kika kawomin gida, and you leave my house kafin nakira bodyguards dina a kulleki” ya nuna Hadiza da yatsa cike da wulakanci kaman kashi yakema magana, Hadiza ga mamakinta kneeling taga Zeenah tayi agabanshi kaman baiwa sai kawai tajuya da gudu sosai fa tawuce motanta da dazu Zeenah tayi parking achan bayan gida sai yanzu tagane mesa tai parking awajen ashe batason mijin yasan takawo wata gida ne tashiga motan da sauri ta tuki tafito around 12:15Am nadare kawai tahau kuka cus from just little abinda tagani dudda mijin Zeenah is a minister tafi Zeenah enjoying rayuwa in every aspect starting from gidama, maybe halan ya ijiye Zeenah a wannan gidan sabida itane Amarya kuma batada yara but still she expect gidan minister yafi gidan mijinta that is into real estate girma da komi amman gidan ta yafi gidan nan da girma da komu har interiors na gidan ta yafi na Zeenah kyau, not to talk of babban gidan da Nura ke gina mata da ba’a gamaba lokacin daya kaita gidan ita kanta saida tai ihu wani kalan design na gini yake da bata taba ganin kalanshi a abujan nan ba, look at yanda Zeenah ke living in fear tun a kotu data cemata zata kwana agidan ta ta lura da wani abu, look at yanda take baiwa in her own house kneeling agaban miji yana fashe fasten utensils agabanki what if tasami injury, sannan bataga yar aiki ko guda daya ba halama batada yan aiki, jibi yanda mijin keta ihu akan me zata kawo wata gidanshi batare data fadamai ba ita look at yanda take kawo kowa gidanta ba ruwan Nura itanema Nura bai isa yakawo kowa bai fadamata ba, Zeenah has been lying to them all this while tana zuga ita da Baraka suci uban mijinsu yanda takeyi so dama karya take, imagine Zeenah data gama zugata dazu harda cemata she’s a disgrace to all feminist out there, look at Zeenah miji ke bossing around yana sata kneeling kaman student, Zeenah dake gayamata taji kunya tana kuka kan namiji look at Zeenah da life datakeyi! Ya Allah! Daidai Hadiza na parking acikin Hilton hotel tadade a mota tai kuka harta godema Allah gash Anty Jams sun kirata bata dauka ba, bawai tana nadaman abinda tayi bane for slapping her da Nura yayi he deserves to be thought a lesson but she’s just hurt yanda Zeenah made her look so stupid and a fool bayan tafita more gidan miji in every aspect dudda tana auren minister, but Zeenah made her look kaman itace the unluckiest wife in history, koda yaushe ji take she wants to be rulling her house kaman yanda Zeenah ke gaya musu tanayi, and abinda ke faruwa is bata cika zuwa gidansu ba cus kullum tana shago kawancen su is suzo shagonta ayi hira a fita, sudanje occasion ko outing that is it, Hadiza batada yawon zuwa gidan kawaye business nata baya barinta saisa batasan actual condition na gidan Zeenah ba, mesa Zeenah zata zugata bayan itane ke facing abuse ma agidanta not she dan Nura bai taba fasa plates a inda take ba, Zeenah lied to her and betray her, tazugata and made her look so stupid, fool, and immature. Hadiza taci kuka ta koshi sannan tafito taje tai booking daki jin kanta na sarawa ta tsani karya da yaudara dan ita kozata mutu bata karya, bata yaudara, bata pretending to be who she’s not, she’s just herself aduk inda zataje a duniya be it to mijinta, relatives nata ko friends natama, ganin kanta zai tsage yasa taje ta kwanta. BECAREFUL WITH FRIENDS MATAN AURE!!!! SOME FRIENDS ARE EVIL!! SNITCH!! ENVIOUS!! WISE!! AND CROOKS!!! Zeenah is just one!!! Now ku fadamin mesa Zeenah tama Hadiza what she did to her??? Please kubani amsan nan! MATAN AURE KUDENA FADAMA KAWAYEN KU MATSALOLIN KU wani zubin daka fadama friends your issues gwara stranger na rantse, bawai ina cewa all friends are bad bane no! But some friends basason suga progress arayuwanki ko cigaba. Dan Allah kubarni nayi this book yanda na tsara nace zan muku magana akan major abubuwan dake kashe aure ayau which the most common one is FEMINISM wanda shine nake nuna muku abubuwan dayake causing arayuwan mu na yau, look at inda Feminism yayi landing Hadiza, this book is not for enjoyment or catching fun novel nope! Idan irin wannan kukeso I have them very tantalizing ma ga dadi check my wattpad page Mshakurworld. This novel is an educating novel dayake nuna illolin of some actions na both side, look at how nake rubuta this book any action na mutum ina nuna how that person thinks and see things, still ina nuna muku idan kina kaza it can leads to this and this and this, this novel is about auren mutum biyu Nura and Hadiza, life nasu, origin na problem din, kaza kaza kaza, I break everything down for you, and I can tell you for free Nura is the origin na this issues for not teaching Hadiza and guiding her as her leader, ya saki Hadiza dayawa, yabata freedom da yawa, saisa hakuri ma da shiru shiru idan yayi yawa is a disease, lokacin dazakace okay bari nafara gyara karfen yariga yanuna harma ya nika, please masu cewa am bias am this and that look at this book from different perspectives and you will see abinda nake kokarin yi. This is a wake up call to all of us mata cewa mu gyara, and this is a wake up call to maza na idan matanku nayi ba daidai ba correct them dan ba soyayya bane dan kayi letting go of mistake na mata infact cutar da ita ma kakeyi indirectly. Anata cewa shi mutum baya chanza wa menene menene, kowa aduniya na da tendency chanza wa either from good to bad or from bad to good, wasu they just have to experience life outside the box kafin suyi tunani, look at Hadiza yanzu just few minutes datayi agidan Zeenah she saw rayuwan wasu couples and tafara tunani this that and this, Hadiza will change guys I know abinda nakeyi but mubarta tayi rayuwan da babu Nura aciki muga how things goes and I sincerely hope you will understand cewa littafin nan nayi shi ne for the betterment of our society in general both daga bangaren mata da bangaren maza Thank you. Allah yamana albarka gabaki daya, yau nabude layina you can either call me or drop a message kota whatsapp kota text 07012181461. Zaku shiga shiga group na matan aure na with just 2k. Chat me up idan kinaso. THANK YOU ❤️ 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣7️⃣ KUJE AGUJE🏃🏾‍♀️🏃🏾‍♀️ KU KOYI HARKAN KITCHEN🏃🏻‍♂️🏃🏻‍♂️ Great news for the people outside jos who are eagerly want to become pastry chefs and bakers. BAKE N’ FROST is bringing you it’s first online class and the class will come with alot of benefits. 🥰🥰🥰 Make sure you join us today. 🤩 Believe me, you won’t regret it because we will be teaching you everything from scratch 💃🏽 ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/Hs8bU0RnXpLA5Lvr1o4qDe Hadiza tajuya nan tajuya chan takasa bacci hakan yasa ta mike tawuce bayi ta tsaya gaban mirror ta wanke fuskanta tana kallon kanta idanunta sunyi jazur, takasa wrapping head nata around abinda Zeenah ta mata, wani kalan daura hannayen ta biyu tayi akan bakinta tafashe da kuka da kyar ta lallashi kanta tafito tadawo daki, wayanta tadauka takira Barakah amman harya katse bata dauka ba hakura tayi ta ijiye wayan ta lumshe idanunta, da ace Zeenah bata ambato zancen court ba da batasa Nuri a kotu ba wlh dudda tasan saitayi bura’uba dashi dan bai isa ya mareta bane ta hakura ba but bazata taba tunanin kotu ba. Zama tayi ta gaban gado tayi shiruu tanaji kaman an daura mata dutse akirji saikuma ta mike tsaye taje gaban wardobe tabude she’s feeling so angry da kanta, duk wacce tace zata iya maka bayanın the feeling after been divorce daga mijinka is just lying dan the feeling is just unexplainable, she’s having different emotions, She’s angry da abu biyu yanda Nura yasaketa yakuma mata iyaka da gidanshi and his life gabaki daya, yanzu fa idan tashiga rayuwanshi yanada hujjan yimata kome yaga dama dakuma abinda Zeenah tamata, takasa gathering courage na kiran gidansu dudda taga kiran Anty Jams takasa dauka takasa kiranta she don’t even know what she’s doing, all abinda tasani is zataci durun uban da uwar Zeenah gobe before she even think of anything dan idan bataci uban Zeena ba bazata sami kwanciyan hankali ba. Komawa gado tayi ta kwanta tasake daga wayanta batasan metake ba but kawai samin kanta tayi da shiga gallery taciro hoton Nura yana sanye da suit da cake agabanshi ranan dayay lunching real esatate company nashi na a Abuja tamai hoton yana murmushi sosai yayi kyau da fararen hakoranshi, Nura is very very handsome, dudda shekaru sun ja but few furfura gareshi kodan yanada kudi ne kuma yana kula da kanshi ga yawan shan fruits but he’s super cute, kuma he’s still very fit bai ijiye wannan pot belly ba. Kuka Hadiza takejinyi tana kallon hoton but tahana kanta yi takasa yardanma kanta tayi kuka sabida wani yasaketa da sauri cikin karfin hali tana kallon hoton nashi cikin wani kalan murya da kasan she’s so hurt tace “ni zaka saka Nuri har kanace amaka shamaki dani who do you think you are? Kana tunanin zanyi kuka ne or I will be hurt sabida kamın haka to nima I don’t want you” tana maganan kuka yazo mata wuya tarike kukan gam tasa yatsanta ta nunashi tace “yesss I said nima I don’t want you, nima amin shamaki dakai, I don’t wanna ever see you” tai maza tai shiru jin kuka na neman kufcemata chan tace “I don’t even know why nake wani tunaka what’s so special about you Nura akwai thousands of men that are way cooler than you’re, sun fika kyau, sun fika kudi sun fika komi so why am I sad? With or without you Nura I will always be Hadiza Mangal Haruna! Babana yabani sunan nan and I will always be that, I have my money, I can give kaina anything danakeso and sponsor any trip danakeso naje so barina dakayi baida any effect akaina kuma kadade baka sakeni ba kaine kai rashi, i promise you bazaka taba samin mata as Preety as I am ba, as loving as I am ba, kuma bazaka taba samin wacce zata baka yara kyawawa kaman wanda na haifamaka ba and lastly Nura saikayi nadaman sakk…….” Kuka ne ya kufcemata da sauri ta ijiye wayan ta daura duka hannayen ta kan fuskanta tace “why am I crying now I hate you Nura I hate you, mugu azzalumi narasa meyake ma mace dayake sa so much effects on her, get out of my heart Nura, get the f*ck outtt already” tafashe da kuka sosai ita kanta batasan why takema Nura wani cool so, he’s just so adorable ne, gentle and cool guys has always been her spec, she loves Nura cus he’s so gently da ita, despite abubuwan dazatamai he will always treat her with so much love and affection kaman batamai komi ba Nura ko is just something else ne kawai a maza, bata taba ganin forgiving man like him ba, baida bakin ciki sannan zai iya sadaukar da rayuwanshi just to see you happy, dudda tanamai iskancin datakemai bata taba fatan ya chanza ba saisa bazatai karya ba daya saketa yau ta girgiza! Bata taba sanin zancen kotun nan zaisa ya saketa ba, abinda yafi jinjigata shamakin daya musu, wato yakai karshe yanzu he’s done with her ohhh no no her heart arching in agony wlh batasan sanda bacci yayi awon gaba da itaba. Wuraren 7 ta farka tashi tayi ahankali tawuce bayi wanka tayi tayo alwala tazo ta maida kayanta tai salla sannan tai order abinci shima tsakura kawai tayi tasake dannama Baraka kira wajajen 8, Baraka na dauka Hadiza tashiga koramata abinda yafaru Baraka tace “mu hadu a shagon ki zan kira Zeenah sai a maida maganan” sukai sallama tashi Hadiza tayi ta shirya wajajen 8:30 tabar hotel room din tana kallon Anty Jams da Mama duk sun kirata taki dauka but taki dauka still hada handbag nata tayi tafito tai checking out ta tafi wajen motarta tabar hotel din zuwa shagonta da har sales girl dinta tabude amsa gaisuwansu tayi ta tsaya ta zabi abaya daya mai shegen kyau tawuce sama office nata dashi tana zuwa ta shirya tsaf ta zauna bata wani dade da zamaba saiga Baraka ta shigo tace “Hadiza” tashi Hadiza tayi cikin fushi tace “ni Zeenah zata yaudara” da sauri Baraka tace “kinga daina ihu Hadiza staff naki na nan” cikin fushi tace “bura’uban staff” fuuuu tawuce kofa tafita tasami yammatan guda biyu tace “kutafi gida nabaku off today” cikeda mamaki suka kalleta ganin da gaske take yasa suka tafi bayan sun mata godiya takoma sama, Baraka tace “Hadiza calm down explain it to me Zeenah tana hanya kinga baban yaran nan nafita nafito nima wlh sabida banma gane maganan dakikemin ba ta waya” Hadiza na kallonta tace “Baraka kinsan halina, ke da Zeenah are my only two close friends duk duniya, Baraka kinsan banda gulma arayuwana tunda nake dake nabata kawo miki maganan wata ko wani?” Baraka tace “a’a zan shaideki awannan Hadiza bakida time din nan” Hadiza tace “bana karya, sannan bana munafuntan mutum wlh yanda abu yake araina haka nake juyeta da bakina, bantaba samin wani naje nabada labarin ki ba, Baraka you and Zeenah are the closest associates danake da shi aduniyan nan banda family na akan me Zeenah zata yaudareni ta ha’inceni” daidai ana bude kofan Zeenah na shigowa tai shigan alfarma tace “kaman ya na yaudareki ko na ha’inceki”? Azuciye Hadiza tajuyo tashi Baraka tayi tace “dan Allah dukanku biyun calm down ku tsaya bari naje na kulle shagon kar customers suzo bamu sani ba” Baraka ta fice da sauri Hadiza da Zeenah sukahau kallon kallo Zeenah ko dar babu tattare da ita saima cingum datake tauna wa Baraka ta dawo ciki kai tsaye Zeenah tace “Baraka kinsan ina mugun ganin mutuncin ki saisa nazo wlh wlh dan banga abinda zai fito dani yau ba dan yau ake zuwa mini full body massage har gida, so why did you call me”? Anatse Baraka tace “Zeenah zauna” takama hannunta ta zaunar da ita akan kujera, Hadiza kuma taja kujeran gaban desk nata ta zaunar da ita tace “Hadiza you too sit please” itama ta zauna Zeena ta zauna kan center table more like tana tsakiyansu tace “we three are friends tun secondary school days namu a college munada n fadan mu da hargowa na yarinta but so far so good tunda mukai aure mukai hankali bamu kara tada ba, please what is happening, Zeenah Hadiza takirani this morning akan kin yaudareta kin ha’inceta, kin kuma cuceta meya faru? Talk to me Zeenah” wani kalan karkada kafa Zeenah tayi ta kalli Hadiza tace “Hadiza ni ne na yaudareki na ha’inceki how? Yan fashi ko kidnappers na kawo aka kwashe kayan shagonki ko me namiki tell me? Ko maganan ki nakai waje? Ni ban kira Baraka nakai karanki ba nida na taimaka miki mijinki ya koraki daga gida nakaiki nawa gidan ki kwana kikahau zagan mini miji saikene keda bakin kice na ha’inceki na cuceki ke babydoll ko, to uwar uban yaya na cuceki ko yaudaranki?” Sosai Hadiza ke kallon Zeenah adah Hadiza feels duk duniya bataga wanda yakaita baki da tsiwa ba, she can stand anywhere and defend herself but yau saitaga batada bakin Zeenah tafita cus for a moment saita rasa mezata fadi na cewa Zeenah ta cuceta ta ha’inceta, tarasa how she will put it in words ayanda takeji azuciyanta sai chan zuciya ya bala’in zo mata wuya amman tadaure tace “Zeenah lied to us she’s not abinda take fada mana she’s, she lied about tanada yan aiki, even vacation din datace taje for her birthday is not like taje din da gaske Zeenah is a crook lier and a deceit, she kept on telling us she’s a feminist ita kaza kaza kaza ce agidan mijinta, she’s lying karya take mijinta treat her kaman garbage, fasa plates agabanta without tsoron kada yaje yajimata ciwo, she’s just so full of lies mayaudariyan mata irin ta, taje tasa na maka mijina a kotu abanza a wofi makira annamimiya la’ananniya kawai, agunguma, wlh Zeenatu ta girmi shedan cus jiya saiya yamata salute din raba aure” jakan dake hannun Zeenah ta ijiye gefenta tana kallon Hadiza tace “ai kinga halin nata bantaba ganin yarinyar mara tarbiya irinki ba Hadiza saisa mijinki ya auro miki yar aikin ki!” zabura Hadiza tayi tamike danji tayi kaman Zeenah ta watsamata garwashin wuta, itama Zeenah ta zabura da sauri Baraka ta tashi tsaye tace “me haka kukeyi, wai ku yarane? Kuna abu kaman masu fama da tashin balaga”? Zeenah tace “Baraka dalla tashi agabana kinada 4kids I don’t wanna injure you for them akan me this stupid girl zatazo tana shararamin zagi ubanme namata, sabida she’s a fool ta dauka because nace ni feminist ce dole sai na dinga zagin mijina kaman yanda takeyi is that what makes me a feminist? Or ta dauka sai na iya ihu da shakemai wuya ina hauka danadenade shine feminist? Muna haduwa and talk about feminism but ban taba cemiki ni ina zagin mijina kuma bana ganin darajan shi kaman yanda kikema Nura ba ko nataba fadin haka Baraka”? Dasauri Baraka tace “a’a” Hadiza tace “amman kina fadamana baki daukan shit din namiji kema kina bashi hot hot, zaman fire for fire kikeyi” dasauri Zeenah tace “Hadiza dakata listen fa kalle ni da kyau ni Zeenatu ce ba Nura ba, stop talking kaman nine nafara saki zama feminist bayan kin rigani zuwa abujan nan ma, dakika dawo garin nan lokacin ina kano ina battling da tsohon mijina kan saki, nadawo Abuja nasameki ayanda kike we just flow together cus we were friends back then and bamu yarda maza su takamu ba so what are you saying?” Hadiza tace “eh amman ke kika zugani nasa Nura a kotu, ke kika sakani daukan that action against him kika kara harda molesting dina yake bayan bantaba gayamiki ba, you are so evil, black witch” Zeenah dake tafarfasa ganin yanda Hadiza ke wanke ta da zagi daban daban tace “you are very stupid for calling me evil and black witch kinji, Hadiza did I hold you at gun point nace saikin sa Nura a kotu eh?” Zeenah tai ihu ahaukace tace “nadauki bindiga na daura akanki nace dole kisa Nura a kotu keda ko maganan Uwarki bakiji wayeni dazakiji magana ta? Kuma molesting bake kika gayamana daya auro Ummi haka yake daddanneki yaciki bakiso ba”cikin tsananin fushi Hadiza na ture Baraka tace “uwata kika zaga?” Cikin fushi Zeenah tace “ke baki zagin uwar wasu”? Bangaje Baraka Hadiza tayi ta taho ahaukace zata damke Zeenah Baraka tasake riketa tana nishi tace “Dan Allah wai me haka ku yarane” Zeenah tace “ko amafarki kada ki kara cewa nina zugaki cus ko uwarki bata isa tazugaki ba balle Zeenatu, bansa gun akanki ba nace kai Nura kotu, dakika bani waya nayi snapping fuskanki as evidence shima nine nasaki? Stupid big for nothing girl kawai, an danna miki saki due to your stupidity yanzu u are looking for who to blame wai I deceive you how? My dear carry your cross kowama yadauki nashi, wawiya kawai da babu abinda tasani banda neman kudi da iya zagin mutane sai kace bamagujiya, ke wlh abin kunyace ga jinsin mu mata cus u are not woman enough tunda kina gidanki har mijinki zai iya yaga yar aikin ki yar kauye yaji yana sonta kin kasa cin bura’uban yar aikin, nine yanzu zakizo with your running mouth kinama hayagaga, if u even try that nonsense with me I will beat nonsense commit for your body niba Nura bane” Baraka tace “wai me haka Zeenah Hadiza kikema magana haka why are you so bitter kawarmu ce fa” Hadiza da Baraka tarike tace “yar bakin ciki dai ba kawar mu bace, bakin ciki take dani wulakantacciyan, gani tayi dudda tana matan minister nafito komi, gida, interiors, kudi, yara and everything” maganan tama Zeenah zafi ainun tace “eh naji but dai tell me cikin abubuwan dakika lissafo wanne yarage yanzu? Yaranki sunfison yar aiki sama dake uwarsu! Same with mijinki ya zabi yar aiki sama dake! Hakama yan uwan mijinki, Shammmmmmeeeee on you Hadiza!” wani kalan zabura da Hadiza tayi tai wulli da Baraka tawani daka tsalle ta zubama Zeenah nushi abaki sai jini, suka shiga dambe ana chakume chakume, ashedai Hadizan mu nada karfi, yau ta haukace tatas ihu kawai take sosai tana kaima Zeenah duka kota ina tace “Shegiyar shedaniya, azzalamu zalumamma, annamimiya miya miya, yar bakin cikin ciniki, ahaka zaki kare, wlh Hadiza namiki fincinkau, celebrate my down fall today your own is coming tommorow” zokaga fadan manyan mata dayake unexpected adiza ta farmata yasa tasami upper hand sai zubama Zeenah nushi dake da kyar Zeenah ta samu ta gannama Hadiza cizo kan breziya saida taji takamo kan nonon Hadiza ta saketa da gudu ta koma baya takama boobs nata tace “vampire witch kawai, Nigerian zombie” zasu koma kan juna Baraka ta shiga tsakiya tace “wlh zan bar shagon nan bazaku kashe juna agabana ba police su kamani” azuciye Zeenah ta tashi ta shiga maida dankwali ta tana share bakinta dake jini da bayan hannu sai haki take tace “kuma Alhamdulillah naji dadi da Nura ya sakeki yakuma miki shamaki dashi dan mace kalanki don’t deserve miji irin Nura, iyayenki ba kowan kowana ya daukoki ya rufamiki asiri ya aureki kinamai iskanci kin dauka bamusan shine yasiyama Babanki mota ba, ya gyara muku gida, sannan ya nemawa mijin yayanki Jamila contract yasami kudi daba hakaba ai a gidanku ke kadai kikadan auri miji me kudi su Rabi ai duk maneji suke agidan auren dan haka yanzu zakisan me rayuwa dan ubanki, business din nan dakike takama dashi saki dinga ciyarda kanki agidanku dan yanzu me ciyarda ku ya sakeki kuma Allah ya kara naji dadi yanda ya sakeki wawiya kawai and welcome to zawarci” tashi Hadiza tayi zatai kanta Baraka ta tareta tace “Zeenah tafi” Zeenah tace “kobaki fadi ba shagon ma ubangiji Allah yasa alhakin Nura ya sauka akai ya lalace, kullum kina mana tunkaho yau acahnxa wannan motan gobe achan a wanchan, Nuri kaza kaza kaza kaman ke kadai ce me miji aduniya you will loose everything banziya kawai karya” cikin wani kalan fushi Hadiza tace “Baraka wlh zan kashe matar nan in batabar min shagoba” da sauri Baraka taja hannun Zeenah itama ta sunkuci jakanta ta fitarda ita daga shagon. Oya registration for shiga matan aure class dina dazai fara November yafara, payment is 2k. Chat me up idan kinaso wa.me/+2347012181461🥰 Hadiza zubewa tayi akasa tasa hannunta aka ta runtse idanunta wacce all her life tadauka as her best friend turns out to be her best enemy, wani irin kuka take mai tsumarai wayanta ke ringing cikin wani kalan muryan kuka tace “Nuri” dasauri ta dauki wayan ganin Babanta ke kira saida gabanta yayi mummunan faduwa, share fuskanta tayi da sauri ta dauka, strictly yace “kada dare tamiki baki shigo gidana ba akano Khadija!” Dip ya katse wayan. Oya registration for shiga matan aure class dina dazai fara November yafara, payment is 2k. Chat me up idan kinaso wa.me/+2347012181461🥰 Wayyyo Hadiza betrayal is painful guys💔💔 Kuna ganin Hadiza ita tajama kanta all this calamity ko ba ita bane??💔 Menene matsalan Hadiza guda daya dakuka lura tanadashi??? Yimata fada akai?? Lemme go first; Hadiza I think kinada yawan zagi, and zagi ba shine solution ba😎 Oya yau mutaru mu mata fada cus ciwon diya mace na y’a mace ne, kufito muma Hadiza fada today 🤗 https://www.instagram.com/p/CyykyCCoKeB/ 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣8️⃣ I am a certified Cosmetologist and I help women of color attain Clean, Clear and Brighter looking skin through supplements. Bari na muku gwari gwari mutanena🤣 itadin certified wato tayi graduating a harkan cosmetologist, kwararriya ce, duk wata matsala dakikeda shi afata tanada maganinta kawai ki sameta, discoloration, kyasfi, dry skin, ke ko baturiya kikeso ki zama zata maidaki yesss😎 kuje page dinta na IG kusha kallo, sannan ga number ta ku danna kumata magana a whatsapp ku fadi matsalan ku. We treat skin conditions like hyperpigmentation, uneven skin, dark spots, skin discolorations and skin aging through beauty supplements that work from the inside. My handle is www.instagram.com/gimigimoraskin Contact Number: wa.me/+2347062972229 28 Ba karamin batama su Nura lokaci akayi ba, shi yana zaune bayan kanta kaman criminal, Alhaji Musa da Lawyer shi ke shiga da fita, ganin yanda suke da kudi aikuwa sun tatsu a hannun yan sanda dan kusan 650k suka kashe wanda duka Alhaji Musa yabiya daga pocket nashi, sannan aka sallamesu Nura yayi signing a some files haka sannan suka baro wajen sukai sallama da Lawyer Nura suka wuce, Alhaji Musa ke tuki bini bini yana kallon Nura, ganin baya iya magana ma yasa yace “nakira Maman Humaira tana gidan tareda su Aman da Amali tun dazu, koda school bus yakawo su already tana gidan” gyadamai kai Nura yayi ahankali, juyarda kanshi yayi yana kallon titi bayako kyafta idanu sunyi nisa sosai ahankali yace “Musa park the car please” parking motan Musa yayi yace “lpy”? Ahankali Nura yacemai “ina zuwa” bude motan yayi yafita yafara tafiya zuwa gefen titi, saida yadanyi nisa sai kawai ya tsugunna yabawa titi baya, Musa dake kallonshi ta cikin mota Nura ya bala’in bashi tausayi dan Nura is hurt da yanda Hadiza ta makashi a kotu dakuma mishi shairi, da wulakanta shi datayi, badadan lawyer shi ba da har handcuff za’a samai a hannu fa, he’s heart broken sosai. Wayanshi daya bari kan kujera ne yahau ruri hakan yasa ya kalli screen din ganin Hajiya ne yasa yadauki wayan tareda saukowa daga mota yawuce inda yake aduke yadafash tareda bashi wayan yace “koma mota kayi waya da Hajiya ita ke kira, bari na shiga super market din chan nasamo mana ruwa, ba ruwa a motan da dan abinci bamuci komiba tun safe” karban wayan Nura yayi yawuce mota tareda zama abaya shikuma Alhaji Musa yawuce super market. Daukan wayan Nura yayi kafinma yayi magana yaji unsettle muryan Hajiya tace “Nura I’ve been calling you tun dazu wayanka baya shiga kana ina” cikeda dauriya gudun kada ta gane komi yace “inda nake ba network ne Hajiya” dan shiru Hajiya tayi jin muryanshi kafin tace “kanin yaron nan dake neman auren Meena yakira yayanshi yake fadi yaganka a kotu matarka takawo karanka shi yana aiki a Admin office ne kaman ku wai dayagani da Meena yasa yakira yayanshi, what is happening Nura? Kaine aka gani a kotu”? Dan lumshe idanu Nura yayi wato babu abinda yakai bad news spreading, jin yakasa magana yasa cikeda damuwa sosai Hajiya tace “what happen talk to me Nura, kasan how worried sick nake kuwa tun dazu nake kira waya ka baya shiga, meke faruwa Nurudeen”? In a very weak voice yace “Hajiya Hadiza takai karana kotu sabida na mareta shekaran jiya…….” Da kyar dai ya iya bama Hajiya labarin sama sama, Hajiya tai shiru kaman wacce ruwa ya cinye tanajin muryanshi dake breaking sosai, ance tsakanin d’a da uwa sai Allah dudda he’s trying to show her he’s fine but she could feel pain din danta piercing through every organ na jikinta, she feel yanda voice nashi is so weak, shaking with lots of sorrow atattare dashi, cikin dauriya da kokarin so tabashi karfi dakuma tsananin so irin wacce mahaifiya kema danta tace “are you okay yanzu? Kun gama zancen kotun? Hope babu abinda ya sameka? Did anybody hurt you Nura? Tell me wani abu yasameka kun gama da kotun, are you fine Son?” Hajiya ya jeromai tambayoyin cikeda damuwa, da tausayi dakuma matukar son danta, baki Nura yabude zaiyi magana sai yaji abu ya tokaremai wuya, dagewa yayi cikin karfin hali irin na maza zaiyi magana yakasa sai hawaye sharrrr, duk yanda yaso ya danne kukan yakasa abinda he can’t remember the last time yayi arayuwanshi sai kawai kukan yashiga flowing, cikin murya mai bala’in rauni da bata nuna kaman mutum na kuka but at the same time kuka yake yace “Hajiya I don’t know why all this is happening to me?” Yadanyi shiru cus muryanshi na rawa kukan dayake yazama so obvious yace “Hajiya Hadiza hurt me deeply, she crushed my ego today, laifine dan na sota? Hadizan danai soyayya da ita harna aura was a hardworking obedient wife, muna dawowa Abuja ta chanza, I put up with every attitude nata cus idan akwai soyayya dole akwai sacrifice da hakuri da juriya, she did so many mistakes ina yafemata and overlook nama manta something like that ever happened, all because of one slap Hajiya wanda in all this years da muna tare ban taba mata ba can’t she forgive me, I am human Hajiya, I get angry too, banfi karfin kofsawaba haka banfi karfin aikata kuskure ba babu abinda fushi baya sawa, but sabida a single slap ta makani a kotu tabatamin suna batare datayi tunani how this action will affect me ba, or my children, Hajiya mata yakamata tazama mai rufawa mijinta asiri, idan yamata kuskure ta rufamai asiri, tanuna min cewa ita ba matan da zata iya rufamin asiri bane and bata damu da self respect dina ba, I love Hadiza alot, I’ve done all I could but tunda abin yakai ga haka gwara na hakura da ita for good!” Hajiya jitayi kaman tayi kuka sabida yanda taji Nura is seriously crying, bazata iya tuna the last time da Nura yayi kuka ba maybe tun yana primary school, Nura grew up as a strong hardworking man, baida magana, ita badadan tazo Abujan nan sabida ciwon taba batasan kalan rayuwan dayakeyi da iyalinshi ba, ko sunzo kano babban salla Hadiza bata zama gidanta gidan su take zuwa to ta ina zata gane wani kalan rayuwa suke ciki? Nura ba gayamata zaiyiba, banda hakama is not proper tasa kanta arayuwan gidanshi, datazo Abuja taga zamansu saisa dayazo mata da maganan auren Ummi bata hanashi ba, saisa take sonshi da Ummi dantaga itane yarinyar dazai iya tankwarawa dan ayanda taga Hadiza wlh wlh tafi karfin danta, babu yanda zatayi ne dan yana sonta amman babu mahaifiyar da zataso taga mata na ganama danta azaban da Hadiza kewa danta, tun ranan farko data shigo Abuja taga kallan zaman dasuke ta dage sosai da yima danta addu’a kan Allah yakawo mai karshen wahalan nan, idan aurensu akwai alkhairi to Allah ya daidaitasu idan babu Allah yakawo musu mafita su biyun. Anatse dakuma soft tone ganin danta is weak tace “Nura bazan maka karyaba auren ku dakai da Hadiza has become toxic, the space will do the two of good, burina shine Allah ya zaba maka abinda yafi maka alkhairi, Allah ya takaita muku wahala, ka kawomin yaran nan kano gobe” kaman maraya Nura yace “tohh” Hajiya jitayi zatamai kuka tadai daure no one can understand the pain of a mother idan taga danta na wahala, Nura is suffering sosai cus yanason Hadiza, Hadiza kuma ta maida Nuran kaman abokin fadanta, Nura yabata tausayi sosai daurewa kawai tayi hatası ta fashe da kuka damuwan takaramai yawa, ahankali tace “kazo kano gobe Ummi na nan wajena” dasauri cikin muryan da ba karfi har lokacin yace “eh”? Ahankali Hajiya tace “Ummi na gidana bataje kauyensu ba” lumshe idanu Nura yayi ahankali saikuma yabudesu baice komiba, Hajiya tace “you will get true this Nura, duk abinda bai ragazaka ba will only make u stronger, rayuwa yagaji haka, Allah ya kyauta ina kuma yima Hadiza fatan shiriya, Allah ya shiryata, Allah ya ganar da ita, sai kazo gobe kaji, Allah tamaka albarka Allah ya rage maka zafin dakakeji azuciyanka, May Allah grant you comfort my Son” ahankali Nura yace “Ameen Hajiya” Ahankali tace “kagama da kotun gabaki daya yanzu?” Gyadamata kai yayi yace “eh ina tareda Alhaji Musa ne zamu tafi gida” Ahankali Hajiya tace “to kuje gidan first I will call u later, don’t forget ka kira mahaifin Hadiza koka turamai sakon message” gyadama Hajiya kai yayi ya katse wayan yashiga aikama Mahaifin Hadiza message dan baijin zai iyamai magana yanzu ba. Hajiya jitayi kaman akwai dutse akan zuciyanta duk yanda zatai bayani bazaku fahimta ba Nura is her only son, shine amatsayin mahaifi ga duka kannenshi mata, shine komi nasu, shine school nasu, shine kayan dakinsu, shine komi, shine abincinta, maganinta daidai da electric bill na gidan nan da swan bottle water datake sha da komi ma shine and Hadiza is trying to kill her son for her, bawai ta tsani Hadiza bane but zuciya batada kashi, datake Abujan nan taga abinda ke faruwa Hadiza ta siremata tatas daga zuciya babu uwar dazatazo matar dake wulakanta mata dan datasan zafin haihuwan shi, Hadiza fitinanniyan mata ce ta fitini danta haba! Aisha takira wacce itace gist partner Hajiya dan banda Nura itace yatta tabiyu kuma kunsan mata da iya relating to pain din maman su. Aisha na kiran Hajiya back Hajiya tafashe da kuka tace “Aisha Hadiza zata kashemini yaro wannan wani kalan abune me d’a yamata? Aisha cikinku babu wacce kema mijinta yanda Hadiza kema Nura, kunama mazanku girki, kuna girmamasu, why is my son so unlucky da mata eh? Kashemin yaro takeso tayi? Zata haifamin waninshi ne eh? Yarona sai kuka yake all because of her, why are so women so heartless? I know babu excuse na marin mace, Nura was very very wrong daya mari Hadiza, mari ba kyau musulunci yahana amman akwai forgiveness a aure, tsakanin mata da miji yakamata akwai yafiya, jinkai tausayi wanda duka naga Nura nama Hadiza, what’s the point na makashi a kotu uban yaran dakika haifa aduniya fa, sabida ya mareki? Idan ma so take abimata hakkinta for marin daya mata she can call me wlh saina sabamai, zata iya kiran mahaifinta takai karan Nura akira amai kashedi kada ya kara taba lafiyanta, kotu all sabida mari is too harsh, so take Nura ya wulakanta aduniya dayau beda kudin bail da yana gidan yari yanzu haka, ga yarinya mai ladabi da biyayya ya aura amman hankali shi baya kanta yafison wacce ke bashi kashi wai yaya kan maza yake ne mesa sun fison abinda ke cutarda su? Hadiza ce kadai mace aduniya akan wani dalili zata dinga wulakanta min da shirun dataga nayi ta dauka tsoron ta nakeji koko ta dauka bansan darajan dan cikina bane”? Cikeda lallashi ganin ran Hajiya na tafarfasa Ya Aisha tace “Hajiya please stop crying is not good for you kada su Meena su jiki suzo suna kuka suna duk hankalinsu yatashi” cikin kuka Hajiya tace “basanan sun tafi lesson din da Meena keyi da ita da Ummi, Aisha I don’t care Nura ya haihu da Hadiza sunada yara all I know shine ko yau Allah zai dauki yara koda Ummi bata karbesu ba ku zaku amshesu bazasu taba wulakanta ba Aman da Amali, wlh wlh idan yarinyar chan takaini bango karshen auren su kenan koda Nura zai maidata saina hanashi, if she’s not ready ta zauna da yarona let her go gabaki daya” calming Hajiya down Aisha tayi sosai, tadinga bata hakuri da kyar tashawo kan Hajiya ta huce tayimata hira har saida su Meena suka dawo gida sannan tabarta tamata sallama. Saida sukai magrib suka wuce gida, Nura na sallama su Amal da Aman dake wasa da yaran Alhaji Musa afalo suka taho da gudu suka rungumeshi suna oyoyo Dady, yaran Musa ma haka boye duk wata damuwarshi yayi yayi murmsuhi suka daddauki yaran suka shigo gidan cikeda girmamawa Maman Humaira ta gaida Nura ya amsa Humaira ma ta gaidashi cikeda girmamawa Nura ya shafa kanta yace “Humaira is now a big girl fa yaushe aka haifi Humaira nazo na dauketa a baby showel a hospital” akunyace Humaira ta rufe fuskanta duk akai dariya, abinci Maman Humaira takawo akaci suka fice dan yin isha’i Humaira ta wanke komi da sukai amfani dashi suna dawowa daga mosque suka tafi gidan yarage daga Nura saisu Aman dake wasa da toys akan rug, dago kanshi Aman yayi yakalli Babanshi saikuma yabar toys din yahayo kan kujeran yazauna kusadashi ahankali yace “Daddy are you fine?” Dasauri Nura yakalleshi saikuma yamai murmushi ganin yanda yaron ke kallonshi yace “yes Dady is fine” dasauri Amal itama tabar wasan ta hayo kujeran ta zauna kan cinyanshi takai hannunta ta taba fuskanshi tace “Dady you look very sad today right Ya Aman?” Gyadamata kai Aman yayi yana kallon Baban nashi shima, murmushi Nura yamusu baice komaiba sai kawai ya kama kansu ya manna musu peck cikeda so, ahankali Aman yace “Dady where is Mom? Bata dawoba” shiru Nura yayi yana kallonsu they have the right susan meke faruwa dudda yarane, anatse yana kallonsu duka biyun dake kallonshi kur kaman tv saikuma yakama hannunsu cikin tsantsan so da kamanta magana ta yanda yara zasu fahimta yace “Mommy will not be living with us again, Daddy is not together with Mommy” Sosai yaran ke kallonshi sukai shiruu dukansu biyun suna kallon fuskanshi chan Aman yace “Momy started doing those bad things again right Dad? Is that why your eyes are read”? Dasauri Amal abunku da yarinyar takai duka hannayenta kan kumatun Babanta tajuyo da fuskanshi saitin nata tawani leka idanunshi kaman wacce ke leka rijiya, cikin muryan yara tace “Mommy hurt my Dad, Aman daddy eyes are red like he criedddddd” taja cried din tana sakin kuncinshi tai kwaba kwaba da fuska zatai kuka da sauri Nura yace “no Amali don’t cry ni banyi kuka ba, Dady ai baya kuka, idanuna na ciwo ne saisa sukai ja” ahankali Aman yakama hannun Babanshi shima kaman zai fashe da kuka yace “Dady I promise I will never hurt you like Mommy does, and we will never ever yelled at you or scream or be stubborn ko Amali”? Gyadamai kai Amali tayi ashagawabe tace “I love my Dady very much Ya Aman I hate seeing my Daddy looking sad” ta rungumeshi, Aman shima ya rungumeshi yace “Dady you are my superhero and I love you alot Dad, you are the best Dady don’t be angry kaji Dady, kayakuri, Anty Ummi said Innallaha….” Dasauri Amali ta taso daga jikin Baban tace “ma’a sabireen” atare suka hada baki sukace “lalle Allah yana tare da mai hakuri, Dady kayakuri kaji” gyadamusu kai Nura yayi yanaji kaman yayi kuka maganansu ya mugun sosamai zuciya kawai ya rungume yaranshi kowanne side side gam gam, arayuwanshi yanason yaran nan, su biyun nan are his soul, yaranshi are just so adorable and sweet kuma suna sonshi sosai, sai yaji Ummi takara shiga ranshi, akwai some small small abubuwa datake koyama yaran da he so much appreciates, kaman son junansu tanunama yaran su biyu are one and Aman should always take care of Amali, wlh dawuya kaga Aman da Amal nafada ko sunyi sharp sharp zakaga Aman ya rungume Amali ya lallasheta he’s so protective of little sister nashi and is all thanks to Ummi da yan tatsuniya da labaran datake basu. Banda haka kana ganin kaman basusan meke faruwa ba they understand everything, saisa ko fada bayaso yanayi da Hadiza agabansu especially Aman dan yaron is very smart. Sun dade ahaka saida yaji dukansu sunyi bacci sannan ya daddaukesu yaje ya kwantar da su adakinsu, wanka yayi anan bayin Aman yafito yaje dakin Ummi yadauko wani jallabiya yasaka yadawo dakin Aman ya kwanta yayi shiruuu sai chan hawaye ya gangaro daga gefen idanunshi dasauri yasa hannu ya share tareda fuzar da iska yace “enough!” Tashi yayi yadauki wayanshi yaciro number Hadiza yayi deleting, yashiga files nashi yashiga deleting komi nata messages, pics, yashiga whatsapp yayi blocking nata ta ko’ina, ya maida settings na wayanshi ta yanda unknown number bazai iya kiranshi ba, yanaso from daren yau yarufe babin Hadiza gabaki daya and just move on with his life, harga Allah he wish her well koba komi itane mahaifiyar yaranshi he wants her to get everything datakeso in this life to tayi rayuwan datakeso, he wants her to excel and attain success in business nata, but for him ya yafe Hadiza koda zai mutu he don’t wanna ever be together da mace kalan Hadiza ma balle Hadiza, he just wanna live his life yanzu da wacce keda opposite of all abubuwan da Hadiza kedashi. Washegari as usual da wuri ya tashi yana dawowa tea yashiga kitchen yamusu yayi microwaving abincin da Maman Humaira ta dafa yayi arranging komi a dinning yaje sama yatadasu ya musu wanka brush yasa sukai salla yafito yabasu abinci tsaf suka cinye daidai wata babban mota na zuwa gaban gidan, sama yakai yaran dakinsu yabasu iPad nasu sannan yafito ya shigo da maza su 7 aka shiga kwashe kayan gidan ana fitar da su, dudda duka kayan gidan na Nura ne, dasukai aure da kayanta aka kawota gidan su na Kano dazasu dawo Abuja yasa ta kyautar da komi yamata komi sabo but he wants her to have it dan Allah yasani da sunanta yasai everything agidan kap, kayan dakin Ummi da gadajen dakin yaran ne kawai ba’a taba ba but hatta kujerun falon sama tass aka fitarda komi gidan looks empty yar kayan kitchen, frames menene menene, address na gidan iyayen Hadiza yabasu a kano yariga yabiyasu kudinsu aka tafi sosai ya tsaya yana kallon gidan da babu komi ciki banda pentin bango, kawai yawuce sama dakin yaran ya shiga yahada kayansu tsaf a akwatinan su dan idan yabar gidan nan sabon gidanshi zasu koma next time, shima ya tattara kayanshi awani akwati yasauka kasa shida mai gadi suka ijiye a boot already yaran sun gama exam badai suyi closing school ba tukunna amman yakira school nasu yagayamusu tafiya takamashi yadawo yadaukesu suka sauko yasasu amota ya kulle gidan yashiga mota office yaje yayi some ayyuka da komi yabarma manager shi aikin sannan by 2:00 suka tafi airport dan 2:45pm jirgin zai daga, yaran were so happy zasuyi tafiya they’ve missed traveling daganan sukai flying sai kano inda direban Hajiya ke jiransu already. Kuna ganin Nura made the right decision na rufe chapter Hadiza gabaki daya in his life?? Koko kuna ganin is not the right decision daya kamata yadauka?? Me aganinku yakamata yayi?? In his statement “I want mace complete opposite na Hadiza” yana nufin wacce is not as educated as Hadiza, expose as Hadiza dadai sauran su, kuna ganin that’s the best thing for him?? What are the perks na auren educated independent woman??🤗 And what are the perks na auren uneducated uncivilized lady???🤗 Don’t forget ku shigo class dina na matan Aure with just 2k chat me up today wa.me/+2347012181461 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 2️⃣9️⃣ https://chat.whatsapp.com/JgukZW7wzUHL8lbg9IraqN INDAI KAYAN SAWAN YARANE TO GA KANKAT NAKAWO MUKU❤️ Do you want your kids to look like those yan gayu kids you admire on instagram? Definitely yes, Eshamin kiddies got you covered. mun shiga mun fita mun tattaro the best for your kids, with chikini money zamu fito muku da yaran ku tass. We make beautiful dresses (rtw and bespoke) headbands and turbans. When it comes to kids fashion you know I no get no 2 You can also check us on IG https://instagram.com/eshamin_kiddies?igshid=OGQ5ZDc2ODk2ZA== 29 Mota suka shiga instead instead sutafi gidan Hajiya direct super market yasa driver yafara kaishi, tsaraba ya kwasa dayawa yakai wajen kayan zaki tsayawa yayi yana kallon roban mentos cingum Ummi ne tafado ranshi sanin tanaci, ahankali yasa hannunshi yadauki roba daya yasa a cart su Aman ma suka kwashi abubuwan dasukeso dukansu yaran were so happy sukaje suka biya direba ya deba yasa a boot suka wuce gidan Hajiya. Yaran sunsan gidan Hajiya sosai ko sunzo salla anan suke zama sai idan Mommy su tazo takan dauke su suje gidan su adawo dasu wajen Hajiya da yamma. Suna shiga gidan Hajiya da gudu suka sauko daga mota sukai ciki, matan dake taya Hajiya aikatu na kayan abinci sai sannu da zuwa sukema Nura dayayi kyau gaidasu yayi cikeda girmamawa ya ciro ragowan cash na aljihunshi yamikama babban ciki su raba sai godiya suke yawuce ciki daidai bakin kofa yaga Hajiya tabude mai hannu rungumeta yayi warmly yace “Hajiyaaaaa” “barka da zuwa Nura, sannu sannu, maraba lale” sakinshi tayi sabida Aman da Amali dasukace “Grandma where’s Aunt”? Gwaggo na murmushi tace “sunje school amman sun kusan dawowa” shiga falon sukayi Nura yasami waje ya zauna yana kallon yanda Aman da Amal ke guje guje suna fadawa kan lumtsa lumtsan kujerun Hajiya falon a gyare sai kamshin turaren wuta yake, sosai Hajiya ke kallonshi yadan rame yafada, yama danyi duhu kadan, kusadashi ta zauna tareda shafa kanshi cikeda so tace “ya kake”? Murmushi yamata yace “I’m fine Hajiya kada ki ramu I’ve moved on” sosai Hajiya ke kallonshi feeling at ease da yanda yayi maganan kanshi ta shafa tace “Madallah, to jeka wanke hannu kazo kaci abinci da kaina namaka girki yau” cikeda kulawa yace “Hajiya bana hanaki aiki ba, me Meena keyi da Um…….” Saiyay dan shiru kafin dasauri yace “all this matan dake tare da ke ai zaki iya sasu koda ace Meena na school” murmushi tamai tace “I cooked for my son, Oya tashi ka wanko hannu kazo, na gyara maka side dinka, idan kuma gidanka zaka sai shima nasa aje a gyara” yatsine fuska yayi yace “banson naje gidan nan Hajiya ina nan, maybe dai naje Adamawa” Hajiya na kallonshi cikeda gamsuwa tace “yakamata kaje kaga Gwaggon Ummi kam” Gyadamata kai yayi kaman ya tambaya ina Ummi yadai shiru yatashi hannu yaje ya wanke duk Hajiya na lurada shi yanda yake kalle kalle he’s just dying to see her, yadawo sosai dagashi har yaranshi sukaci abincin Hajiya kaman wayanda suka fito daga yunwa tass yagama ya mike yace “bari naje na watsa ruwa a side dina” Hajiya dake bawa su Aman abinci abaki da hannunta tace “toh” wucewa yayi yafita yataka zuwa wani side dake dan nesa dana Hajiya babba ne flat din, bude kofa yayi yashiga an gyara falon dayaji komi sai kamshi yake yawuce bedroom ga akwatinshi har ankai ciki, ruwa ya watsa yafito ya tsaya ta window yana goge jikinshi daidai nan yaji yaranshi na ihu ihunsu yacika gidan. “Anty Ummiiiiiii” dasauri yasa hannunshi yadan dage labulen ya leka, Ummi yagani sanye da dogon rigan abaya black mai shegen kyau ta yane gyalen akai dayadan zamiye baya ana ganin kitson datayi ma shuku yan kanana masu kyau hannunta dayasha jan lalle rikeda jaka haka dayaga books aciki tawani daga Amal da bala’in mamaki takasa yarda yaran ne kaman Hajiya bata sanarda ita zuwansu ba. Tsayawa Nura yayi chak yana kallonta she look peng, way prettier than before, black skin nata nawani kalan sheki though idanunta sun fada ciki but she looks thicker than yanda ya santa, dan lumshe idanu yayi yana kallonta yanda harta daura Amal abayanta ta rungume Aman ta gaba suna juwa juwa matan gidan na musu dariya, jiyayi zuciyanshi ya buga! Kasa daina kallonta yayi she looks sooo happy da ganin yaran suma yaran haka, saida yaga da ita da su sun wuce dakin Hajiya sannan yasaki labulen window idanunshi kaman zasubi Ummi falon. Suna shiga falon Ummi ta gaida Hajiya tace “Hajiya yaushe su Amali sukazo”? Murmushi Hajiya tayi tace “dazun nan da Baban su sukazo yana bangaren shi, yaje yadan watsa ruwa” faduwa gaban Ummi yayi daman zuwanshi yasa Hajiya takira aka mata kitso da lalle kuma tabata wasu magunguna jiya da daddare tasha dabata san na me ba, yayma da safe har wani farfesun kaza aka bata taci da wani maganin, amugun kunyace takama hannun Amali tace “kuzo muje dakina” itama Hajiya cikeda hikima tace “jeki ajiye abubuwan school kizo kici abinci ku shiga kitchen ko, mijinki yazo gari ke zakimai girki” gimtse dariya Meena tayi Ummi kuma akunyace tace “tohh” tawuce dakinta su Aman na biyeda ita kaman bindi, deep down jitayi takosa tadaura Nura a ido amman kuma fushi take dashi, but she’s just so happy yazo kanon, she missed him alot, salla tayi ta chanza kaya zuwa wani atampa mai shegen kyau sabo ne ma am mata gown fitted daidai jikinta shape nata yafito sosai tasa dan kunne tana kokarin yin dauri Meena ta shigo dakin saikuma ta saki baki cikeda tsokana tace “biki zaki ne Ummi”? Cikeda rashin gane tsokanan tace “bikin ina”? Murmushi Meena tayi tace “ohh kenan duk yayana akema kwalliyan nan ai na dauka fushi kike dashi”? Akunyace Ummi ta nuna su Amal dake wasa da wayanta tace “me haka Meena yara na nan fa” hararanta Meena tayi tace “ni zauna namiki daurin” zama tayi tamata daurin tai kyau sosai kaman ba kitchen zata shigaba ta shafa turaruka, takalli kanta amadubi saitaji tanama kunyan Hajiya ta ganta ahaka Meena tace “muje” dasauri Ummi tace “Meena mesa nai gayu haka girki fa zanje nayi ai Hajiya saitamin wani kall……” “Ummiiiii” Hajiya ta kwala mata kira da sauri tace “na’am” tabi gefen Meena tabude kofa da gudu tafito kawai taci karo da mutum zata fadi yariketa da sauri ajikinshi suka tsaya chak suna kallon fuskan juna but jikinsu amanne da juna, sosai Nura ke kallonta yana sanye dawata soft milk yadi mai shegen kyau yazo kiran Aman suje masallaci Hajiya tace “yaje yana ciki” yawuto nan, da gangan Hajiya ta kwalama Ummi kira dan so take su hadu, lumshe idanu Nura yayi jin wani la’anannen ni’imantaccen kamshin datakeyi dayamai sallama a hanci feeling her soft skin da hannunshi daya na waist nata daya nakan hannunta ta wajajen muscles, he miss every part na jikinta kaman yar baby yarike ajikinshi haka yaji yakasa koda kwakkwaran motsi sai zuciyanshi dake bugawa, almost 30secs sukayi ahaka suna kallon juna babu wanda ya iya magana cikinsu, da kyar Ummi ta iya samun natsuwan fita daga jikinshi cikin wata yar muryan da ita kanta batasan tanada shi ba dakeda kaudi asirace tace “iiiishhhh sorry Baban Aman ban ganka ba” bata jira amsanshi ba tabi ta gefenshi tawuce tana wani irin cat work dake juya ass dinta, wani kalan automatic baci alwalan Nura yayi wow! Yafadi cikeda mamaki irin is this Ummi yanda tamai magana casually kaman ita dashi basu taba sharing any relationship ba, kaman irin ta yafeshi arayuwanta din nan wai sorry Baban Aman ban ganka ba, kaman banda shi Baban Aman ne batasan wani matsayi nashi ba awajenta, fitowa daga dakin da Meena tayi yasa yajuyo da kanshi dasauri yakalleta tace “Yaya kaine” “call Aman” Nura yafadi kai tsaye, dasauri Meena tace “sunachan suna wasa da wayan Ummi bari na kirasu” dasauri yace “don’t worry jeki” yawuce yashiga dakin wayan Ummi ya karba daga hannunsu yasa a aljihu sannan yace “suje” saida yakara komawa side nashi ya dauro alwala sannan suka tafi, basu sake shigowa gidan ba shida Aman sai bayan sallan isha’i. Around 9, yana shigowa dakin Hajiya yabi dakin da kallo ganin baiga Ummi ba sai yaji ranshi yadan baci, gaida Hajiya yayi, Hajiya tace “akawo abinci Nura”? Dudda bayajin yunwa at all dan yaci abinci dazun din nan dayawa but ahankali yajuya dan baiso yahada ido da Hajiya yace “akawo side dina Hajiya kaina ciwo yake zan kwanta” yana maganan yafice murmushi kawai Hajiya tayi kasa kasa ta kwalama Ummi kira tafito tana sanye da hijabi har kasa sai kamshi take kaman sabuwan amarya Hajiya tace “hada abincin mijinki ki kaimai side dinshi kekuma Meena bawa Aman abincin shi yaci karyay bacci baici abinci ba” Ummi batace komiba tawuce babban kitchen na Hajiya wani tray tadauko mai kyau tazo dinning ta jeramai duka lafiyayyen abincin datamai hade da juice data hada faduwa gabanta yayi tadan juyo takalli falon taga Hajiya bata falo itada Amal sunyi ciki Aman ne kawai zaune yana kallon cartoon a tv yana jiran abashi abinci kaman daga sama Meena tai whispering mata a kunne “kina fita zan rufe kofan falo, bamuso ki kwana anan yau, kiji kuyi bura’uban ku shirya” dasauri Ummi ta kalleta tace “wlh kada ki rufe kofa anan zan kwana mezanyi achan”? Keya Meena ta sosa tacigaba da abinda take na dibanma Aman abinci, Ummi tadauki tray din tawuce tafita tana tafiya ahankali hakanan gabanta sai faduwa yake har zuwa gaban kofan flat nashi, tsayawa tayi tadan sauke ijiyan zuciya ta daidaita numfashinta daya hargitse sannan tasa hannu tai knocking, daga ciki taji calm voice nashi mai dadi dake nuna natsuwanshi yace “come in” sake sauke ijiyan zuciya tayi ta hade giran sama da kasa sannan tabude kofan ahankali, zuba mata mayun idanu Nura yayi dudda talura da yanda yake kallonta but taki kallon inda yake tawuce ta ijiye abincin akan coffee table dake gefen kujeran dayake kai ahankali Nura sai bin kafafunta yake da kallo dan iska na daga hijabinta har santala santalan melanin cinyoyinta yake hangowa, kaman karamin rigane ajikinta ma, harde kafafunshi yayi he just desperately wants a woman dan ko kadan baida natsuwa a tattare dashi, and yanzu daga ganin Ummi abin ya tasomai, tashi tayi bayan ta ijiye tray din tajuya zata tafi kai tsaye yace “Ummi!” Chak ta tsaya har cikin bargon kashi ta taji muryanshi da yanda yakirata, batare data juyoba tace “kana bukatan wani abu ne”? Authoritatively yace “dawo ki zauna” dan juyowa tayi ta zubamai manyan idanunta cikin harshen turenci tace “why?” Yana kallonta shima fuskanshi ba wasa yace “sabida ni mijinki nace ki zauna” wani kalan kallo Ummi tamai da bata taba sanın zata iyamai ba tace “ohh au, hakane ashe inada miji! Ni badan ka tunamin ba na manta fa Baban Aman” Sosai Nura ke kallon kwayan idanunta mamakinta na kasheshi, anatse tace “bazan zauna ba” tajuya zata wuce tashi daya Nura yayi azuciye ya fizgota kaman zaki saida Ummi ta firgita dasauri takalleshi tace “me haka”? Yariga yayi alkawari mistake dayayi akan wanchan matan (Hadiza) yagama bazai kara bari mace ta wanashi ba and get away, he is the husband and he will control kowa, yana rikeda ita yasa hannu ya murza key kofa yacire key ya jefa a aljihu yawuce yana rikeda ita ya zauna kan kujera, kaman zata fashe da kuka Ummi tashiga turashi tace “nika sakeni nawuce natafi” cikin kakkausan murya Nura yace “anki din sarkin zuciya” fizge fizge Ummi tashigayi zata kwace kanta daga jikinshi amman takasa tace “nika sakeni kabudemin kofa nawuce natafi nahakura da auren ka tunda yanzu banda wani amfani awajenka” sosai Nura ke kallonta bai taba sanin ta iya rigima da bori hakaba saiyay, sai mutsu mutsu take da hijabi hakan yasa kawai ya yaye hijabin ya yar a kujeran next to them, arude Ummi tafashe da kuka tace “wlh zan kira Hajiya nagaya mata abinda kakemin” saura kadan yayi dariya yabi kitson kanta da kallo dayay kyau sosai ya sauko jikinta tana sanye da wani red night gown iya cinyanta mai spaghetti hand very transparent, daurewa yayi yace “tashi kibani abinci naci yunwa nakeji tunda kukan banza kikejin yi, Hajiya Ummi mai zuciya bazan lallasheki ba mara kunya kawai” makemai kafada tayi tace “ai kanada hannu baram baka abincin ba” saura kadan yayi dariya yanda tai maganan kaman wata Amal tana kuka still, yace “zanyi maganin rashin kunyanki fa, tashi kibani” sake makemai kafada tayi tana komawa baya akan jikin nashi, yunkurowa yayi dasauri ta tashi tace “to zan baka ai” komawa yayi yazauna itakuma ta bude kulolin tashiga zubamai a plate tanajin haushin yanda kaman baimaso suyi maganan fadan, boobs dinta Nura ya tsare da ido dan yanda ta duka tana deban abincin he could see everything sunan wani bera wai bubbling bunny, every motsi da zatayi na deban abinci suma saisunyi, he was just having dirty thought picturing breast milk na fitowa daga nipple din zai zuba a abincin kawai yazo yatara baki, dan lashe lips dinshi yayi her nippi are succulent, wani kalan ijiyan zuciya ya sauke ba shiri yadauki throw pillow yasa saman kafafunshi yacigaba da kallonta dauko plate din tayi tazo tana turomai baki tazo gabanshi tabashi karba yayi zata juya ya fizgota jikinshi kaman mara stamina tafado, kankameta yayi sosai for the first time yasamu ya rungumeta da kyau he really miss her kasa fita daga jikinshi tayi kaman yamata magani sai taji jikinta ya mutu murus yanda ya kankameta yana buga bayanta ya mika dayan hannunshi ya ijiye abincin kan table, cikin wani cool calm voice dake cikeda lallashi yace “am sorry for hurting you Wife, I take full responsibility for actions nawa which I believe damuwa da rashin natsuwa da rashin baccin kirki yasa nayi abinda nayi but bazan taba wulakanta ki ba Ummi ki fahimce ni, you are part of me already nidake mun riga munyi sharing bond din ma’aurata, haba Ummi ina miki kallon mai hankali da natsuwa sai kawai kiyi zuciya kiyi tafiyanki kinsan kalan yanda raina yabacı kuwa? Kinsan kalan damuwan dana shiga? Akanme zakiyi tunanin banda bukatanki ko bani sonki ne? Kowa da matsayinta araina ko kene in that condition haka zanyi, but baki jirani ba koda laifi namiki ki gayamin kawai kika tafiyanki saikace karaman yarinya, but kiyakuri please banson fadan nan dakikeyi dani kinji, kibani kwanciyan hankali Ummi” makemai kafada tayi alamun “a’a” hannunshi yatura a aljihu yaciro mentos yace “koda nabaki cingum bazaki hakura ba”? Dasauri tadago kanta ta kalli cingum din hannunta tasa dasauri zata amsa yadaga hannunshi sama chan dasauri ta kalleshi tana turo baki tace “ni kabaniiiiiiiii” shima ashagwabe yayi maganan yace “ni tashi ki amsaaaaaaaa” dasauri ta tashi akan cinyoyinshi tawani mikarda hannu zata amsa da gangan tai wani smacking booby nata akan fuskanshi ta mika hannu zata amshe kaman wacce batasan metayi ba ashagwabe tace “ni kabani abunaaaaa” lumshe idanu Nura yayi yabude bakinshi ahankali yasa tongue nashi ya lashi nipples nata dake sosamai fuska tasaman riga, dasauri takoma ta zauna akan jikinshi ta turo baki tace “bani cingum dina” ahankali yana kallonta yabata, amsa tayi tai wani murmushi mai kyau tareda budewa taciro daya tasaka abakinta tana lumshe idanu sai kallonta yake, murya chan kasa idanunshi na kukkullewa yace “Ummi sonake na sadu dake soo bad” kallonshi tayi da sauri tana kallon kwayan idanunshi da basa buduwa da kyau, cikin wani mugafalin murya Nura yace “sonake na murza tumaturan kirjin nan naki na fashe su na shaye” dan lumshe idanu Ummi tayi da sauri tsigan jikinta na yirrrrrr sabida yanda yayi maganan, cikin tsananin sha’awa yace “bani hakki na Ummi, amugun bukace nake dake, inaso ki tatseni tasss yanda kika sabayi, ki cire gajiyan nan daga jikina Baby kiyi miyan dagedage dani” yayi maganan yanakai hannayenshi duka jikinta zai tabata chak ta rike hannunshi tana kallon fuskanshi hakan yasa shima yadan kalleta da idanunshi da basa buduwa da kyau kaman zai fashe mata da kuka yace “ba mun shirya ba”? tana kallonshi itama kaman yanda yake kallonta tace “sona kake Nura ko sha’awata”?. Kuna ganin Nura nada feelings for Ummi koko sha’awa ce kawai??? Yanzun dai tayi miyan dagedagen dashi ko kartayi??😎 Send message today and join NOVEMBER matan aure class with just 2k💃 07012181461 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR BONUS💃 Kowacce mace tauraruwace🤩,amma kasancewa hakan ba abu bane mai sauqi. Kinada bukatar inganta rayuwarki ciki da waje tare da inganta rayuwar aurenki. EXCLUSIVE SABAYA BY A²🌾shine mafi dacewa, sauqi,da Kuma kyau don inganta lafiyarki tare da inganta rayuwar aurenki. EXCLUSIVE SABAYA BY A² 🌾ta zama zahra don kuwa duba da yadda hadin ke gyara mace ciki da waje sama da kasa tare da inganta lafiyarta hadi da inganta rayuwar aurenta. Wannan hadin shi akeyiwa kirari da cikakkiyar mace👠Daga cikin amfanin wannan hadi akwai:- ✓ Gyara nono ko samun ruwan nono lafiyayye ga mace mai shayarwa(lactation support) ✓ Kayan gyaran aure💞 ( Aphrodisiac) ✓Makon abinci ko sinadarai da jikin Mace ke bukata don inganta lafiyarta ciki da waje da Kuma rayuwar aurenta🌿 ( natural wellness product) da dai sauransu. Abin burgewa da wannan hadin🌾 babu ruwanki da dame dame Kunu, ruwan dumi kawai kike bukata da cokali daya na garin Exclusive sabaya by A²☕😋asha safe da maraice. Muna maraba daku matan arziki🤩Mallaki naki cikin sauqi 👇🏼👇🏼👇🏼 https://wa.me/2347032698888 Facebook/Instagram Asquare Beauty and More Wlh saida gabanshi ya buga bumm! Dan yaune rana na farko da Ummi ke kiranshi Nura direct tunda ya santa is either ta kirashi da Baban wane, Dadyn wane, My Noor ko Alhaji, yadade yana kallonta kaman yanda take kallonshi itama, dan lumshe idanu yayi yace “mesa zakimin kalan tambayan nan”? Tana kallonshi tace “sabida zuciyata tanada bukatan sanin amsan” tadanyi shiru kafin chan tace “bawai ina fushi dakai bane, but banson rayuwana ta baci abanza bayan ba sona kakeba har yanzu ni yarinya ce, zan iya samin mai son……..” wani mugun kallo da Nura yamata sai kawai taji maganan ya makale awuyanta tana shakkan tafito dashi, dan sha’awa yana sha’awan Ummi sabida she makes him feel like a man wani zubin itane ke tunamai yanada gaba ma na saduwa da mace, that aside he loves her because of so many things, he has grown attached to her, and he’s so fond of her kuma, data tafin nan babu ranan da baya tunata kawai dai yasan son dayakema Ummi daban son daya kema wanchan matan (Hadiza) daban yafadi aranshi yana kauda tunanin Hadizan da sauri daga zuciyanshi dan ijiyan zuciya ya sauke kafin ya karbe hannunta data rike yakai saman soft face nata yadaura yana kallonshi cikin wata gamshashiyan murya yace “ina sonki Ummi kuma ina sha’awan ki sabida ina sonki” dudda yanda yayi maganan yana wani shafa fuskanta kaman yar yarinya yasa taji jikinta ya mutu amman daurewa tayi ahankali tace “pru-bit (prove it)” tafadi tana kallonshi dan dan school din nan dasuka fara zuwa itada Meena tafara koyan turenci kallonta Nura yake cikeda sochan yace “tayaya kikeso na shaida miki ina sonki da gaske”?Dan turomai baki tayi ashagwabe tareda make kai tace “ni kada ka nemeni harsai naji ajikina kana sona saini in nemeka” sosai Nura ke kallonta dan yanzu babu abinda yake nema ido rufe kaman samin natsuwa wlh kaman yaci kanshi haka yakeji barinma dayaga Ummi sai yaji lissafin yasake kwance mai, abu ya hadiye awuya mai daci da kyar yace “shikenan, are you happy yanzu”? Gyadamai kai tayi kaman yar yarinya tace “beri beri haffi (very very happy)” tawani dauki cingum dinta tareda gyara zama akan cinyanshi tajuya tana facing tv tabashi baya tasa cingum daya abaki tana lilo da kafa gently tanadan motsi da ass dinta akan cinyanshi exactly yanda yara keyi idan sukahau kan kafafunka sujuya suna activities nasu, ijiyan zuciya Nura ya sauke yanaji kaman zaiyi ihu sabida yanda soft ass nake ke caressing laps dinshi, bayanta yabida kallo dakenan so smooth ga gashi abayan wuyanta akwance, saukar a gaze dinshi yayi down zuwa inda rigan bayan ta baya yafara he could see cikin bayanta yanda babu komi ciki, bai gama tunanin ba Ummi tawani kwanto jikinshi kaman yanda yara ke kwantowa tadaura kanta saman hannunshi taki kallon fuskanshi idanunta nakan tv tana chewing cingum tai lakur kaman mussa ahankali tana murmushi tace “laaa Dadyn Amali kaga nushin dayamai awuya” tanuna tv, ina Nura jiyayi kaman ya danneta awajen, bin tundaga face nata zuwa chest dinta yayi da kallo, her nipples were damn hard sunyi wani kayau kayau arigan irin jiran tumurmusa kawai suke, lumshe idanu Nura yayi ahankali yace “Ya Ilahi!” Dasauri Ummi tajuyo da kanta ta kalleshi tace “mekace?” Girgiza matakai yayi yakasa magana, tashi tayi daga kan jikinshi tamike tsaye tadan kwanto ta saman jikinshi slapping his erected D da boobs nata trying to carry hijab nata dake kujeran next to wanda sukekai tace “zan tafi” rawa kafafun Nura suka fara kaman wanda yaji shock kuma yake shirin sakin fitsari, dasauri Ummi ta dago tasa hijab din aranta tana mamakin wani kalan sha’awa yakeji haka da har kafafunshi ke bari saitaji yabata tausayi amman tadaure tace “saida safe” cikin muryanshi datadan dishe yace “tsaya nazo na rakaki” tashi yayi yawuce bayi ahankali Ummi jitayi kaman tai kuka wlh tana bala’in son Nura sama da tunanin ta, kawai so take yamata son datakemai shima, kusan 2min yayi yafito gaban jallabiyan still atashi amman kaman yakamata da boxer so tarage girma, yazo inda take tsaye yamikamata hannunshi alamun tazo kaman bazatazo ba sai kawai tazo sata yayi ajikinshi ahankali wani dadi da Ummi taji har zata kankameshi saikuma ta hana kanta tafito daga jikinshi dan ijiyan zuciya ya sauke kana ganinshi kasan karfin hali kawai yake yace “let’s go” binshi tayi suka fito atare suka jero babu kowa compound din sai wuta ako’ina har kofan dakin Hajiya da suka gani akulle, har kasan ranshi Nura yaji dadi kuma yasan aikin Hajiya ne, dasauri Ummi ta taba kofan tace “waya rufe kofan”? Ta bubbuga shiru babu wanda ya amsa tattaba jikinta tayi tunawa datayi bata taho da wayaba yasa da sauri ta kalleshi yana kallonta facial expression nashi ya nuna jin dadi, ashagwabe tace “ni kakiramin Meena tabude min kofa” yana kallonta yace “sunyi bacci bazan tada kowa ba, muje chan ki kwana awajen” yajuya abinshi knocking takarayi ganindai kaman sunyi baccin yasa tajuyo tana tafiya ahankali kaman bataso but har kasan ranta taji dadin yanda zata kwana adakinshi she miss mijinta over, mugun sha’awanshi takeji dakuma so yatabata but tanaso taja aji, haryakai flat dinshi ahankali take tahowa yana tsaye yana kallonta yanda every step kesa boobs nata shaking lurada abinda yake kallo yasa takai hannunta gaban hijabinta ta dage sama sabida ya dena mannewa ajikinta yana mata kirji. Tana kaiwa gaban dakin bude mata kofan yayi yana murmushi ciki ciki wucewa tayi ta shige shima yashiga tareda maida kofan yarufe ciki kawai tawuce abinta tana juya ass yabita da kallo kaman maye yayi murmushi yana mamakin sabon tafiyan iskancin nan data koya aiko bazai bari tadingayi awaje ba, ya kashe komi na falon yataho cikin bedroom, bata ciki but ga hijabinta akan lafiyayyen gadon dakin, that means tana bayi da gangan ya cire kayan jikinshi, yadauki hijab din nata da rigan baccin ya linke yabude wardrobe yasaka yawuce yabude bayin kai tsaye ya shiga Ummi na tsaye kasan shower tana watsa ruwa kawai taganshi ba kaya ya shigo da sauri ta duka tace “me haka Dadyn Amali?” Kaman baisan yayi wani abuba yace “menayi”? Yayi maganan yana daukan toothpaste yana budewa ya matsa akan toothbrush zaikai baki yace “hurry ki gama wanka nakeso nayine” baki Ummi tasaki ganin iskanci wai irin shi adole baisan yayi komiba dinnan yashiga brush abinshi, binshi tayi da kallo asace daga sama har kasa wlh yanada very nice skin, there’s this thing about elderly men da bazata iya fadi ba is just in aura nasu, sauke idanunta tayi kan D, he’s still having wani angry erection awajen ware idanu tayi tana kallon joystick din da kyau saitaga kaman yamafi da girma, it’s looks so juicy, jitayi she’s dripping, she just want that stick inside her, ganin kaman da gangan yake mata har wani kara karkacewa yake sabida tasami good and perfect view na abinda yaga tana kallo da gefen idanu hakan yasa itama tawani mike abinta tashiga kasan shower tahau wanka tana shafa jikinta da gangan tace “aaaaaassshhhhhhh” wani kalan juyowa Nura yayi ya kallonta da brush abakinshi jin lalataccen moan din datayi, wani kalan mikarda wuya tayi tana running hands nata ajikinta baisan lokacin da kumfan toothpaste yafara fitowa daga bakinshi ba, saida Ummi taga yagama shagala akallonta sannan tawani jaaa towel ta yafa ta kashe shower tafito tana tafiya ahankali kaman hawainiya Nura nabinta da kallo ganin yanda Ummi ta iya act of seduction, yanda kasan wata K, saida tazo dab dashi tawani kwance towel din tayafamai akafada cikin muryan jaririya tace “ga towel dinka” tawuce tafice Nura yanda kukasan Mumu sai kallon ass nata yake da he just feel like spanking cus basuda manners🤣 Maranshi har wani ciwo ciwo yake sabida jaraba. Yan turarenshi data gani ta fesa ajiki kawai ta wuce tahau gadon ahaka batasa kayaba Allah yasani tafasa jan ajin nan she can’t lie so kawai take Baban Amali yacita, wlh tai kewan abun ya iya, babu abinda takeso irin taji wannan abin acikin jikinta barinma dazu dataganshi abayi sai kawai taji ta manta lissafin dake kanta, itadai Allah ya dauramata son abun Baban Amali wlh dadi, ga abun yar fara fara kaman shi, kuma ya iya lalubeta kaman yaje makarantan lalube da sakucen mace, Anty nashan dadin nan ya akayi take iya fada dashi? It’s gashi so take tai fadan takasa sabida so take taci, burinta kawai yamata, ya iya matseta da mata wasu kalan abubuwa, so kawai take suyi, dama dayaya take bacci kwanan nan, bargo kawai taja ta rufa tana mammatse cinyanta mugun sha’awa takeji dazu ashema batajin komi yanzu ne takeji fitowanta daga bayi fa Kenan but harta jike, ijiyan zuciya ta sauke ta kalli kanta tareda sa hannu taja duvet din kasa kadan sabida boobs nata daya yafito danta san Nura naso, so take yakasa hakuri kawai ya nemeta ita wlh tafasa abinta tace dazu, haba ina ai saita mutu, hakanan itada mijinta wlh ba’ama abin dadi yanga, zata iya wani fushin banda na harkan wawatsula, jin yana kakorin bude kofa bayi yasa tawani lakur achan karshen gado daga ita sai bango ga boobs daya yafito daidai Nura yafito turus ya tsaya ganin Ummi kwance ta rufa he could see half na left booby nata awaje ga that dark nippi awaje areola sun tattare kaman kayan da za’ama tie and dye, hannunshi yakai da sauri ya shafa maranshi ina wlh saidai Ummi tace sha’awan nata idan baici yarinyar nan da daddaren nan ba to ko saidai in yamutu, yafadi yana yarda towel akasan wajen yasan mezai mata ta manta komi har kanta yanzun nan, ya danna wutan bangon dakin ya chanza ya maidashi zuwa deem blue light yazo ta gaban gadon ya tsaya, hannunshi yasa ya yaye bargon racing zuciyan Ummi yashiga yi, cikeda jaraba yasa hannun yawani jawo kafafunta zuuuuuu ba burki ta taho yana landing duka both legs din nata a shoulder nashi dasauri Ummi data bude ido tace “alkawarin me kenan”? Cikin muryanshi da bata fita da kyau yace “alkawarin mu na nan bazan nemeki ba, amman ai zan iya wasa da jikin matata” yayi maganan yanabin thighs nata datake kai hannayenta tana rufewa da kallo ganin how wet ko’ina yake ya kalleta yayi murmushi turo baki tayi tace “miye? Ni ka saukemini kafafu daga kafadan ka” ahankali yanakai bakinshi thigh din yace “bari namiki tsarki tukunna” tongue nashi ya daura kan right thigh din yawani licking down to V, zabura Ummi tayi arude ta daura hannunta da sauri takama kanshi gam tace “Baban Amali zubarudun dadi nakeji…….kadenaaaaaaa!!!!, fuskanshi yakai daidai V din gabaki daya dudda blue light ne but wajen was as smooth as baby’s type, cikin muryan da bata fita yace “zubarudun dadi kikeji”? Arude tace “uhn, uhn wlh” yace “kinaso nadena?” Tarude tace “a’a kacigaba ko in maka kukaaaaaaaa” tana magana yanda kasan aljanan baby ne ta shigeta, wani vertical zulbe yamata awajen har wani tustus vijay yayi na numfashinta Nura yace “bani hakurin zuciyan dakikamin kikabar gidana kona dena” as usual tariga tai loosing 5senses nata tace “Dadyyy natuba baran karaba I chuweeww” Nura yace “you swear”? Tace “uhmmmmm to kacigaba da shaminnnnnnnn” maka bakinshi Nura yayi kaman zai zuko born marrow daga kashin rago, Ummi tahau ihu…… 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣1️⃣ JuiceVillehub Tigernut drink naturally made and very rich and creamy(Kunun Aya mai dadi da babu kamar shi). So refreshing da zaki sha kiji dadi a baki kuma kiji a ciki😉.Sannan kuma ga fresh fruit juices naturally made suma da zaki sha su gyara miki skin inki kiyi fresh. Muna yin single order na yau da kullum kuma muna yin na events for your guests to make that event a memorable one. Ga instagram handle inmu da WhatsApp link. Ig handle @ Juicevillehub.ng Link https://www.instagram.com/Juicevillehub.ng Whatsapp http://wa.me/2347018944377 Call 07018944377 31 Waiwaye baya kadan! 5:00 daidai jirgin su Hadiza ya sauka a kano, fitowa tayi ahankali gabanta sai faduwa yake da maganan Baba, hakanan ta tare taxi 5k yakaita harchan Dakata dan anan gidan su yake, wani madaidaicin gidane yanada gate haka baki, gidan daidai na rufin asiri, sauka tayi tabiya kudi tajuyo gabanta still na bugawa tabude gate tashiga gidansu, kayan dakinta data fara gani a tsakar gidan yasa kawai taji wani irin chills na sanyi na shiga jikinta kawai ta tsaya chak tana kallon kayan, wani abu taji ya tsaya mata awuya amman ta daure ta danne tadauke idanunta dagakan kayan tafara tafiya compund nasu nada fadi gawata hadaddiyar Camry golden dake pake a compound din, babban flat ne guda daya agidan sai bq tabaya daga labule akayi aka fito Rabi ce rikeda kwano a hannunta ganin Hadiza yasa tace “Anty Hadiza, Mama Anty Hadiza ta iso” ijiye kwanon tayi da gudu tai wajen Hadiza sai kawai ta rungumeta tace “Anty Hadizaaaa” fitowa Hafsa tayi da gudu da babynta ma a hannunta amman ta ijiyeta tazo da gudu sai kawai suka rungumeta, Hadiza jitayi jikinta yamata wani kalan sanyi kafafunta kawai sukahau tankwashewa da kansu daidai Anty Jams da Mama nafitowa daga dakin, kallo daya Mama tamata tace “ku shigo da ita daki” kakkamata sukayi Hadiza takalli Maman nata dake mata kallo irin kallon haushinta takeji sosai din nan tace “kin sami abinda kikeso ai shikenan, ga gidan ubanki nan saiki zauna, ku wuce ku kaita ciki nace” Mama tai maganan with so much annoyance Anty Jams tayi shiru tana kallon Hadizan wacce idanunta kadai zaka kalla ta baka tausayi dan sunyi zuru zuru ta wajigu, wlh dudda tana fushi da Hadizan amman tabata tausayi matuka kaman tamata kuka, wucewa da ita ciki sukayi zama tayi a falon Rabi ta kawo mata ruwa da gudu kadan tasha kawai ta ijiye Mama da ranta ke masifar abace dan ba dadi auren yarka ya mutu wlh babu, balle kuma auren da kasan diyar naka ne at fault sai bakın cikin yazaman maka guda biyu, gana mutuwar aure, gana yar cikin nakane taja, no mother wish for mutuwan auren diyarta. Sallama akayi wani magidancin mutum Ustaz sosai fa yana sanye da babban kaya da hula akanshi mai rawani yashigo gidan da wani mai kama dashi wanda zaka gane kaninshi ne, shiga falon sukayi Hadiza tasauke kanta kasa dasauri ahankali tace “ina wuni Baba” wucewa Baba yayi ya zauna kaninshi a gefenshi ya zubama Hadiza idanu kana ganinshi kasan yanada dan zafi irin ba mutum mai sanyi bane, babu wani bata lokaci ya nuna tundaga kan Jamila, Mama har zuwa kan Hafsatu yace “dago kanki ki kalli yan uwan ki kinsan mesa dukansu ke gidan nan yau”? Kasa dago kanta Hadiza tayi gabanta na faduwa sosai dan tana shakkan mahaifinta matuka tace “a’a Baba” cikin tsananin fada yace “sabida dukansu harda mahaifiyanki sukasa hannu suka tayaki kashe auren ki! Akanme kina gidan mijinki shekara da shekaru dabi’un banza kike zubawa banda labari?” Yayi maganan da fushi yana daga murya kowa ya sauke kanshi kasa cikinsu yace “akan me? Uhn uhn uhmmm Amadu kwanakin baya da diyar nan tai rashin lafiya cemin akayi rashin lafiya ne kawai, mijinta yace duk suje abujan yaturawa Jamila kudin jirgi sabida ciwon zuciya likitoci sunce tana bukatan yan uwan ta abinda aka gayamini ke nan, anyi haka ko ba’ayi haka ba”? Baba ya tambayi Mama data gyadamai jiki asanyaye, Baba da ranshi ke tafarfasa yace “saida sakon bawan Allahn nan Nura ya shigo wayana yace Baba namaka laifi na mari Hadiza abisa kuskuren fushi dakuma zafin zuciya wanda nai nadaman hakan, ta shigar dani kotu anbi mata hakkinta, Baba kayakuri na saki Hadiza saki nabiyu yau, yoo banmasan sanda akai na dayan ba, amman Mahaifiyarta da Yayarta da kannenta sunsan komi sukai shiru suna kallona saida na sami Maman na titsiyeta take gayamini gashi, gashi, gashi, ai yanzu gatanan tadawo gida kun huta”? Yayi maganan yana kallon Maman Hadiza yana bubbuga kafa akasa yana tafarfasa yana nuna musu Hadiza da hannu. Cikeda tsantsan adama da danasani Maman tace “Malam kayakuri, na amince namaka laifi, amman ka fahimce ni, iyaye maza sunada zafi barinma kai saisa zaka gani yawanci iyaye mata kan boye laifin yaransu daga mahaifan su gudun bacin rai da fushi, sa’an nan na dauka fadan damuke mata dani da Jamila zataji ta dauka basai ka shigo zancen ba, kaga kuma ada bahaka Hadizan takema komawanta jarababben shedanin garin nan ne yasa taje tahadu da shedanun ciki itama ta rikida tazama daya, amman kayakuri Malam, na dauki kuskure na hakan bazata kara faruwa ba, kayakuri Malam” “hakuri bayan kun kaso mata auren?” Baba yayi ihu yana hargowa dayasa Maman Hadiza ta runtse ido cikeda jin dacin maganan shi, Baba yace “Amadu Allah shaidane kaima shaidane yarana nabasu tarbiyan boko da islamiyya, dukkan su nan har ita Hadizan babu wacce batai sauka ba, nabasu tarbiya, sunsan Al,Qur’an, Tajweed, Tafseer, Ahalari, bulugul maram, umdatul Ahkam, zuhudu, fikihu, not to mention others, kai ni nan dakaina saida na zauna na koyar da yaran nan kap dinsu littafin siffofin mar’atul saliha, na killace su nakuma tabbatar da na aura musu mazaje nagari amman mahaifiyar su kullum boye mini zancen yarana take” Maman Hadiza tace “Malam kayakuri” dan shiru Baba yayi saikuma ya kalli Hadiza yace “kalleni ke kuma dan kaniyanki” ahankali Hadiza tadago kanta gabanta nafaduwa dum dum dum sosai takalli Baba, da hannu ya nuna kanshi yace “tunda na haifeki kin taba ganin Mahaifiyarki tamin ihu?” Girgizamai kai Hadiza tayi ahankali, cikin tsananin fada da kumfan baki Baba yace “kintaba ganin ta gasamin magana koko kin taba ganin ta rainamin wayau, ke kin taba ganin Mamanku tace nine zan muku girki yau ko na shiryaku zuwa makaranta koko kintaba ganin ta zauna tace ita tagaji da aikace aikacen gidana yau nine zanyi bani amsa” Baba yabuga hannun kujera, girgizamai kai Hadiza tayi, cikin wani kalan fushi Baba na kallon Hadizan dake girgizamai kai yawani zabura yatashi daga kan kujera kaman zai daketa yace “kin taba ganin mahaifiyarku ta daukowa Gwaggo yan sanda kafin ta rasu”? Tashi Hadiza tayi da gudu tawuce bayan Mama tariketa gam jikinta narawa gani take kaman dukanta zaiyi, akwai wani kalan haiba da kwarjini da mahaifinsu kedashi kodanshi Malami ne oho, amman baki isa ki kalli idanun Baba kiyi hayagaga agabanshi ba, babansu baida wasa ko kadan, sun taso shiba uba mai wasa da yaranshi bane saisa tsoronshi ke jikinsu tun suna yara, tsakaninsu dashi yakoya musu karatu yabasu abinda suke bukata but irin wasan nan kaman yanda Nura keyi dasu Amali ina Baban su baya wannan at all. Dasauri Amadu yakama Baba yace “Yaya dan Allah kayakuri kaga Hadiza ba yarinya bace dazaka daka ba, magana kadaima ya isheta” ture Amadu Baba yayi yace “Amadu kasan hukuncin wanda yaci mutuncin iyaye kuwa? Matan nan ina kwanakin baya kafin taje Abujan saida nidakai mukaje har gidanta muka maidata, Hadiza matan dake ciwo kusan kowa yasani hawan jini da ciwon sugar sun sata gaba, ke har Mahaifiyanki da Jamila suma sunje sun gaidata, amman kika zagi Matar nan, kuma sabida rashin da’a kice bazata sauna gidanki ba, sannan ki dauko mata yansanda, tunda muka haifoki mun taba tsinemiki ko muntaba miki bakine dan wannan dabi’un tsinannun yara kikeyi wayanda iyayensu suka yafesu su shiga duniya su adddabi jama’a, muntaba tsine miki ne Hadiza”? Hawaye ne suka fito daga idanun Hadiza masu zafi. Maganganun Baba na mugun tabata dudda bawai tsinuwa yake mata ba but yanda yaketa tsinuwa kalman sun tsinemata ne har cikin kwanyanta takejin kalman, Baba ya fizge kanshi yanuna Amadu yace “ka kara rikeni saina kwada maka mari” yazo wajen Mama kawai ya fizgo Hadiza daga bayanta dasauri daga Mama harsu Anty Jams zasu saka baki Baba yace “Wlh babu ruwanku, duk Wanda yace tak sainayi mummunar sabamai” yarike hannayen Hadiza gam takasa kwacewa ido cikin ido dan abinda tama Hajiya ya girgizashi da aka fadamai yau, yace “Hadiza kin isa, kinkai matsayin yau, kawai so nake ki nunamin kin isan, da karfin ikonki da mulkinki dan haka yima ni ubanki duka” yakama hannayen Hadiza yakai saman fuskanshi zai mari kanshi da hannunta, da gudu Hadiza ta dunkule hannunta tawani kalan fashe da kukan da tuntuni take rikewa tace “Babaaa” cikin tsananin fushi Baba yace “Wlh, wlh, kinji na rantse miki saikin dakeni yau dan abinda kikama mahaifiyar mijinki yamafi dukan nan dazakimini ni mahaifinki girma Khadija, yafishi sau dubun dubara, uwa zaki daukoma yan sanda, ki kirata dakikiya, matan nan ta girmeni ni mahaifinki amman comfortably kika zageta, sannan saida kikasa tafita tabar gidan dan da ta tsuganna ta haifo, mareni! Dakeni nace me kike jira yimin duka” yanda Hadiza ke kuka ta dunkule hannunta gangam taki bude palm din kar Baba ya mari kanshi saiya baka mamaki, Baba yace “ai wlh baki isaba kinyi abinda yafi wannan yanzu kuma kice bazaki iya dukana ba, I said beat me” azuciye Baba yakai dunkulallen hannun Hadizan ya buga afuskanshi da hannun da kyau fa bawai duka kadan ba, wani kalan ihuuu Hadiza ta tsandala arazane irin tayi wani babban tabooo dinnan ta daki mahaifinta ta fizge hannunta dagana Baba daya sassauta rikon yana kallon reaction mata ta tsugunna da gudu tana wani kalan kuka tana goge hannayenta da gudu ajikinta irin ka rude din nan kayi laifi da hannunka kana purifying nasu immediately, Baba ya tsaya chak yana kallonta idanunshi sunyi jaaaa cikin wani kalan murya mai sanyi kaman kankara yace “how do you feel yanzu dakika dakeni ni mahaifinki? How Khadija”? Yayi tambayan kaman kankara, kasa magana Hadiza tayi sai goge hannun take tana kuka abun yay shaking nata ainun, Baba ya jinjina kai ya nuna kofa yace “Khadija kinma that poor old sick woman abinda yafi dukan nan dakikamin just now, cus ni mahaifinki just a physical punch kikamin but ita kin mata emotional, mental and even physical one din” yayi shiru sai kawai ya juya yakoma kan kujera ya zauna tareda daura hannayenshi akan fuskanshi jikin kowa yayi sanyi har ita Hadizan ganin mahaifinta na kuka, kowa was just cold a falon, fadan Baba ya taba jikin kowa, Hadiza jitayi kaman Allah yarigama ya jefata a wutan jahannama wannan kukan da dukan datama mahaifinta. Yadan dade ahaka kafin yazare hannunshi ya goge idanunshi tass dasukai ja yace “kaico! Wallahi Billahi duk wanda ya wulakanta iyaye baya samin karshe mai kyau! Khadija yau na zubar da hawaye akanki sabida nariga na sani ne tabbas sai anwa diyata, diyar cikina abinda tayi ma wasu kama tudini tudan Hadiza!” Har wani shock Hadiza taji ajikinta maganan Baba ya shigeta, Baba yace “ana wani zamani da mata da yawa basason iyayen mazajen dasuke aure sun tsanesu, sun maidasu kaman wasu makiyansu, shi soyayya ba dole bane amman kyautatawa da sauke hakki dole ne! Yau koda bakason wani kada ka cutarda shi, da Hajiya bata haifa Nura ba dazaki sami Nura ki aura?” Baba yamata tambayan tasauke kanta kasa ahankali, shiru yayi yace “Khadijahh Annabi SAW yace Man tashabbaha bi qaumin fahuwa minhum, that whoever imitates others, he will be from amongst them duk wanda yaso wasu to yana tare dasu, kinje Abuja kin kaunaci dabi’un da mutanen dakika samu awajen sunayi to ranan gobe kiyama tare Allah zai tadaku” Baba yayi shiru yana kallonta chan yace “aure bautane, Allah yafadi acikin Al Qur’ani mai girma; “وَمَا خَلَقۡتُ ٱلۡجِنَّ وَٱلۡإِنسَ إِلَّا لِيَعۡبُدُونِ” “Wama Khalaqtul Jinna Wal Insa Illa liya`a buduun, And I have not created the jinn and mankind except that they should worship Me, Ban halicci mutum da Aljan ba saidan su bauta mini. Hadiza part of bautan Allah shine aure amman kikai auren but bakiyiba, kikaje kinama ma mijinki abubuwa daban daban” Baba yasakeyin shiru kafin yace “Nura mutum ne, dan idan nine matana ta zagi Gwaggo na kota dauko mata dan sanda basaki daya zan mataba aurena da ita har abada mungama na hakura, kinsan waye iyaye? Kinsan girman iyaye da darajan su? Fushin Allah yana daga cikin fushin iyaye hakama yardansa, idan iyayenka suka yarda dakai Allah ma ya yarda dakai, Aljanna Nura na karkashin kafan iyayenshi, bakiso ya rabu da su lafiya? Sabida kin tsani mahaifiyarshi karya kawota gidanki? Karya nema mata magani who are you?” Baba yasake shiru yace “mari ba kyau ba kyau ba kyau! Ke kinma bawan Allahn nan kuskuren dayafi na mari bai miki ba, kuma ya yafemiki, zaman aure zomu zauna zomu sabane, kowa na kuskure a duniya, akanme bazaki iya yafemai kuskure dayan nan ba tak! Kika makashi akotu kin riga kinma sunanshi tabo har karshen duniya!” Baba yasake shiru na kusan 5min Chan yace “Abu biyu zuwa uku zan gayamiki, abinda kikayi kunya bazai taba barina na nemo Nura na muku sulhu ba bani acikin zancen nan idan yazo Alhamdulilah idan baizo bama Alhamdulillah!” Baba yayi shiru chan yace “abu nabiyu shine idan ada kin kada ganyenki kin tashi sama kin baza reshe bada sanina ba yanzu na shigo lamarin nakuma san meke faruwa bazan taba barinki ki koma Abuja ba saidai idan mijinki ne yazo ya daukeki daga gidan nan nawa ya maidaki!” Dasauri Hadiza takalli Baba dan business dinta kawai take tunani yace “daga rana irin tayau ko gaban gate na gidan nan bazaki kara zuwa ba idan kinga kin fita daga gidan to kin gama idda ne!” Hadiza takara kallon Baba gabanta na faduwa yace “kin riga kin nunama duniya gabaki daya bakida tarbiya, iyayenki basu koyamik, sannan ke gantalalla ve kuma tijararriya ba? To remember this shi karatu is never too late duk girmanka kuwa dan haka zaman gidan nan tarbiya ni mahaifinki zan koya miki da kaina! Dakaina Hadiza dan har mahaifiyar ku ban yarda da itaba yanzu” Baba ya sauke ijiyan zuciya yace “kinga duka abubuwan da bakiyi agidan mijinki ba starting from gobe dasafe kin farashi kennan!” yanda kirjin Hadiza ke bugawa zaka sauka gangan ne ake bugawa aciki, Baba yace “girki na safe, na rana dana dare na kanki, sharan tsakar gidan nan da gyaran gida, wankin kayan mahaifiyarki nawama sa’a kikaci wanki da guga nake bayarwa, wanke wanke da wankin bayi, bayan haka kullum ni da ke ina dawowa daga sallan asubar kullum ranan duniya zan karantan dake littatafai daga Alifu ba’un zan fara miki dan naga kaman kin sami memory loss duka kwakwalwanki ya shafe, komi da kika iya da yabace Allah yasama kin iya karanta fatiha yanzu” Baba yayi maganan da kakkausan murya sannan ya nuna Hadiza da yatsa yana kada kafa strictly yace “kinga dokokin nan dana shimfidamiki idan kika karya daidai da guda acikin su na sallamaki daga yaran dana haifa kenan aduniya” azuciye Baba ya tashi yana gyara Babban Riga shi yace “Amadu tashi mutafi masallaci” baima jiran Amadun ba yafice ranshi abace, Hadiza tafashe dawani kalan kuka sosai mai tsuma jiki, Anty Jams ba karamin dadin hukuncin baba taji ba shine daidai da Hadiza dan tana ganin ma maybe taurin kan Baba Hadizan ta dauko, ai zaici kaniyanta yanzu juyawa tayi kawai tace “Mama natafi gobe zanzo kuma ku wuce kutafi” tama su Rabi’a magana kozata lallashi Hadiza not today let her feel the gravity of mistake datai commiting tukunna before tamata magana but tabata tausayi kuka takeji but bataso tayi yanzu saita fita tashiga mota she pity her sister sosai. I cried for Hadiza today😭 But ya kukaga hukuncin mahaifinta??? Yayi daidai ko yayi tsauri?? https://vm.tiktok.com/ZMjpou6Ex/ 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣2️⃣ Kuna neman AFFORDABLE KAYAN BACCI DA BREZIYU, hohohooo gafa Qawxars nan💃 ku riketa gam gam and thank me later🥰 Are you looking for where to get affordable and quality sleepwear and underwear from the uk? Look no further @qawxarscollection got you covered we have alluring and beautiful bras padded and non padded, matching sets, sleep dresses, pj’s, & gift packages. What are you waiting for? Check us out on Instagram https://instagram.com/qawxarscollection?igshid=OGQ5ZDc2ODk2ZA== Or click to send a dm wa.me/+2348032022128 32 Tana cikin kumbure kumburen ya sallame sallan hada ido sukayi ya zuba mata matattun idanunshi dake kashe mace farare tass dasu yau sabida yasami natsuwa dawani kalan sauri Ummi ta dauke kanta ranta abace sosai azuciye ta yunkura zata tashi taji bata da karfi jikinta duka yayi tsami kaman ba nata ba, hakan yasa ahankali alallabe ta tashi tareda jan bargo tana kare jikinta ita adole karya ganta, sauka tayi gently zata fara tafiya tai luuuuu zata fadi da sauri Nura yataso yatareta yana kaita jikinshi with so much affection yace “bakiga bakida karfi ba” kallon fuskanshi tayi yayi wani kyau da haske suka hada ido takasa magana, murmushi yake mata kasa kasa hakan yawani kara kular da ita dawani kalan sauri ta turashi ta dago tace “ni kadena tabani mekamin ma jiya”? Dan zaro idanu Nura yayi duk yanda yaso yarike dariyan dayakeji kasawa yayi saida yadan murmusa kadan wani kalan kulewa Ummi tayi cikin rigima sosai kaman yaron daya tashi daga bacci afusace tace “kamin wulakanci tunda nabar gidanka baka taba nemana ba, shine daga zuwanka jiya bansan me kaminba har kamin wani abu ko” tsayawa Nura yayi yana kallonta shi dariya abin ke bashi yadai daure yarike dariyan, Ummi tace “dariya kake ko to baruwanka dani, kada ka kara kulani nagaya maka” tana maganan tawuce bayi tana tafiya ahankali tana faman jan bargo saida takai gaban bayin tasaki bargon tashige ciki. Sai alokacin Nura yadan saki dariya tareda murmusawa sosai irin na manya ya kadakai, all he sees kawai is tsantsan yarinta, he loves childishness nata sosai abun is so cute, zuwa gaban kofan yayi ya daga bargon yazo ya yaye zanin gadon da sun bata tass yaciro wani ya shimfida, yatafi falo yadauko hijab din Ummi, yabude cikin kayanshi yaciro mata wani boxer nashi da singlet duk ya ijiye kan dadduma sannan ya zauna yana lumshe idanu komi najiya nadawomai sabo fil arai, ranan datamai massage yace that was the best sex in his life but yanzu yana ganin na jiya was just the best omoh Ummi can f*ck and puss nata come Sweet, saikuma tazo ta iya ihu da batsa ahhh full package! Murmushi yayi yakai hannunshi saman jallabiya wlh har gabanshi yafara mikewa, yarinyar nan is so turning him on, fitowa tayi daga bayin daure da towel kanta duk ruwa taki kallon inda yake sai kumbure kumbure take, cikeda so yace “ga shimi da boxer kisa saiki salla” batare data kalleshi ba tace “agaban ka zansa kayan? Ni kafita” ba musu yamike shi adole mai neman sulhu yace “toh My Madam” hanyar falo yayi yabude kofa yafice tadanyi murmushi yanda yamata biyayya ya burgeta, kayan tasaka tasa hijab tai salla tana idarwa tai azkar sannan ta tashi tabude kofa tafito falon Nura na zaune yaganta ganin zatai kofa yatashi yakamota cikeda rigima tace “stop kadena tabani” hade fuska yayi yace “kin gaidani”? Dan kallonshi tayi gabanta yafadi kafin ahankali tace “ina kwana” bakinta ya kalla tsabagen kiss da shan dick har sun karaja, hannunshi yakai gently ya shafa bakin yace “bakin daya iya batsa agado” dauke kanta tayi dasauri akunyace, yakai hannunshi ya shafa goshinta da gashi dayawa sun kwanta cikin wata kalan yar mitsitsiyar murya yace “ina sonki Zainab” wallahi har kasan zuciyanta taji kalaman nashi tadauke kanta da sauri tace “ni zan tafi” yana kallon long eyelash dinta yace “saina karbi hakki na tukunna Yammatan Nura” dasauri takalleshi ganin shi baimasan kunya ba saima gira daya ya daga mata gabanta yafadi adan shagwabe kaman ita yace “waiba mun shirya ba me kuma nayi da safiyan Allah din nan amarfi namiki laifi”? Fari Ummi tamai da ido saikuma kawai ta fashe da kuka dake kashe zuciyan namiji cikeda so Nura yakamata yana tafiya da ita ya zaunar da ita akan kujera ga mamakin ta sai kawai ya duka agabanta tareda kamo hannunta ahankali yace “Zainab nasan sabida yanayin circumstance na auren mu you feel kaman bana sonki, bana girmamaki kokuma bana darajaki duk ba haka bane” yadanshi shiru yana kallon yanda take share kukan datake da bayan hannun jijiyan goshinta na fitowa alamun she’s really hurt da yanda bai nemeta ba abin yaki fita daga ranta and so yake yafitar dashi yanzu, murya chan kasa yace “banson mufara rayuwan auren mu a wannan yanayin Ummi da ace bana sonki da bazan taba aurenki ba dan bazan taba, kalli bakina bazan taba iya auren wacce ban so ba wallahi!” Yafadi ahankali, yace “Ummi tunda nake arayuwana bantaba growing feelings for mace in few days kaman keba, da lura dake da falling for you took me just few days that’s to show you how special you are, duk macen dazan iya fadawa soyayyanta dumu dumu cikin dan kankanin kwanaki is a very special woman, Ummi you are a special girl” yayi dan murmushi yana kallon yanda take kuka da duka zuciyanta saikawai yatashi yace “come here” kaman jira take da sauri ta rungumeshi bayanta ya shafa yace “I am really very sorry for hurting you, abinda kikamin yayi matukar batamin rai ne Ummi yanda kikamin zuciyan nan, abin yacimin rai yakuma sosamin rai, i need to correct you na nuna miki ba’a haka saisa nai shiru na kyaleki but dudda haka nakasa daurewa haka nadinga kiranki wayanki akashe” dan dago kanta Ummi tayi cikin kuka takalleshi tace “da gaske”? Gyadamata kai yayi cikeda tausayinta dawani kalan kaunanta ganin yanda ta ke sonshi yace “wallahi da gaske Ummi, harma muka shirya nida Musa zamuje Adamawa mu daukoki but something happen daban samu na jeba, but kiyakuri kinji” gyadamai kai tayi ya saketa ahankali gaban tv yaje yadauko tissue yadawo da kanshi ya gutsuro yakai hancinta yace “huro majinan” kallon idanunshi tayi saita huro tafashe da wani kukan looking so emotional sai hankalinshi yatashi yace “Ummi mena miki haka kike kuka is getting serious kinason kisani damuwa ne?” Cikin kuka sosai tace “Baban Amali ina sonka sosai saisa kome zakamin yake tabani, tun bayan Mamana da Babana sun rasu na wahala a hannun mutumin nan da Gwaggo tazo tarabamu dashi, yana zuwa gida yadakeni nida Gwaggo ina kwance ina rashin lafiya kullum jinake Allah yakawo wani rayuwana wanda zai soni, ya killace ni daga hannun mugun nan, ya adana ni yanda Babana zaiyi idan yana raye cus babana yana sona” tasake rushewa da kuka tace “Allah yasani ban aureka danna cutarda Anty ba, inason Anty inason yaran data haifa, kawai zuciyata ta aminta dakai, sabida kanada hankali, ka darajani ka girmamani, gaka babba nasan idan ina taredakai ina tareda kwanciyan hankali, inaso nazama matarka ina zaune karkashinka, da abin yafaru sainaji kaman banda rabo aduniya kaima baka sona shikenan banda kowa” awwwn Nura jiyayi idanunshi sun cika da ruwa da sauri ya tsayar dasu yadago fuskanta yace “Ummi ina sonki sosai bazan taba wulakanta ki ba wlh, badan na wulakanta ni na aureki ba, zuciyana nada fadin dazata iyaso Mata hudu, lokacin hankalina atashe yake kuma I see you kinada understanding ban dauka zaki fushi ba saisa nai haka Ummi, but na gane kuskurena tun alokacin ma da Hajiya ta sanar dani, Ummi mata na miji na samun sabani but communication shine ke warware sabani, kome zan miki kada kiyi zuciya ki banni ki sameni ki gayamin mu tattauna akai kinji” gyadamai kai tayi saikuma gently tai kneeling agabanshi ahankali tace “kayafemin kuskuren dana maka na zuciya da rashin fahimtarka danayi Baban Aman, bazan karaba dagayau” tsayawa yayi yana kallonta the way she’s kneeling saikawai yaji this is what you call a wife! Da sauri yaduka ya dagota yace “nayafe miki, nima kin yafemin, i hurt you my baby, nasaki kuka harda majina, kuma kinyi kuka sosai lokacin ko?” Gyadamai kai tayi kaman yar yarinyar tace “idanuna harda kumbura” dasauri Nura yakama kunnenshi yace “auuuchhh tuba Nura yake, an karbi tuban ko za’a bani punishment” dasauri tai murmushi tana cire hannunshi daga kunnenshi tace “nayafe ma Mijina kuma ina sonka sama da rayuwana Noor” murmushi yamata yajawota jikinshi ya rungumeta so tight, sun dade ahaka yace “I will be taking you on a date anjima da daddare, soyayyan dabamu samu munyi kafin muyi aure ba da kyau yanzu zamuyi agidan Hajiya, jibi zan koma Abuja zan barku nan zanje duba gidan mu upper week kotasaman zamu koma gabaki daya, yanzu jeki shirya zan kaiki for shopping na kaya dan anjima da night gayu nakeso kici sosai, zakije shopping”? Gyadamai kai tayi dasauri, yace “yauwa, daganan zan kaiki Bank kibude account akwai wasu kudade danamiki kyautan su a hannuna” yadagota yana share mata fuska yace “jeki shirya gani nan zuwa nima, I love you” ya mata peck akunyace tawuce tafita ranta fesss saikuma ta juyo takalleshi suka hada ido tace “bayan mun dawo da daddare zan maka suprise wawatsula!” Wlh kalman saida yasa gaban Nura ya harba dasauri yakai hannunshi wajen yakama yana kallonta yace “zo kifadamin anan menene wawatsula” dariya tayı tana make kafada tace “nizakama wayau ka danne nagaji bye mijin Ummi” tamai gwalo tareda bude kofa tafice da gudu Nura yayi dan dariya ya kalli abin yace “kaikuma kai hakuri mana ance anjima za’amana suprise wawatsula”.🤣 Shopping yamata na ban mamaki, daganan sukaje bank abokinshi ne take yanke aka bude mata account ya zuba mata miliyan biyar dakuma 2m extra, 1M na ranan tazuge 1M na jiya, Ummi saida ta rungumeshi a bank tana realle bata taba ganin kudi hakaba haka suka dawo gida Hajiya sai dadi takeji ganinsu. Bayan isha’i harda Hajiya da Meena aka shiga shirya Ummi that was going on a date da Nura, Hajiya takawo gold bangles nata tasama Ummi a hannu ta sanya wani red lafiyayyen gown Meena tamata makeup su kansu yaran sai cewa suke Anty Ummi kinyi kyau kiranta Nura yayi awaya hakan yasa Meena tace ”tashi kije yana mota” kasa tashi tayi sabida Hajiya, Hajiya tai dariya tace “tashi ni kafin na kwadeki gulmamma” akunyace Ummi ta tashi tafito tana tafiya kaman hawainiya, Nura saukowa yayi daga jeep din Hajiya yafito yana kallonta kaman yau yafara ganinta, su Hajiya da girmanta sai leke suke ta window harda yaran fa kaga abu, wayanahi yaciro yace “wait lemme snap you dan kinyi kyau matan Nura” yana murmushi yamata hotuna sannan yasata amota ya maida yarufe suka wuce hannu Hajiya tadaga sama tace “Alhamdulillah Ya Allah ka dawwamar da farin ciki arayuwan su” Meena tace “amin”. Omoh jama’a love sweet wen money enter is sweeter cafe gabaki daya yayi booking Nura. Anyi arranging an zuba flowers suka shiga Ummi sai murmushi take bata taba ganin kalan abinba, abinci daban daban ake kawo musu da wanda ta iya ci da wanda bata iyaciba bayan sun gama aka bawa Nura speaker zaiyi karaoke ya karba yana kallon Ummi yace “yau zan miki wakan soyayya Ummi kin shirya”? Gyadamai kai tayi tana murmushi sai yatashi ahankali yadan tsaya nesa da table daidai ansa wakan but volume din is soo low ta yanda idan Nura zai bi muryanshi za’afi ji, yadan fara motsi da kafa in a very classic way yana bawa Ummi wani love look chan ya lumshe idanu kafin yabude su kadan ya nunata da yatsa yafara” “Ina kewa, Ina kewar masoyiya, Ina kewa, Ina kewar aminiya, Abokiyar shawara, Ke ce kin dara, Kin san inba gake ba, Sai in hakura, Ki bani yar dama, A san da ni nima, Ki mini alfarma ki sanya ni a zuciya, Ki kauda yan gulma, Irinki ke nema, Suna ta shan fama, Sun zaga ko ina Mace ba aiba kece, A ido riba kece, Kuma kin san mundace, A kanki na zauce, Magana daya (ba shakka), Bude kanjin ka, Ta ya-ya zai dauka Samun ki baiwa ce, Bakya fushi, Ki murmushi, Dan sanki na shiga rai na Ko ba ni in kinka tuna ni wannan shi ne muradi na, Nasan kina da buri Kuma sannan kina da tsarin ki, Da zaki sa cikin ran ki nine zan zama angon ki, Farar tumfafiya ta daban cikin mata, A sanki nai rata a kanki na gane kaina! Kece naiwa alkawari, Mace daya kuma kin zarce dari, Kinzam min bangon sikari ko a ina kece, Sirrin ciki yazo fili, Kin iya ado da dan kwali, Mai kyan ido da sa kwalli, An iya maki zanen lallai, Tunda na sameki na huta Saura sun ka kazanta Bana iya kallon mata kiji kalmar da na furta Akwai dadi abun da kakeso in ya so ka!……. Ummi kawai sai kuka, staff suka bata tissue ta karba da sauri tana goge idanu tana kallon Nura she felt love, taji soyayyan shi in every part of tissue and born na jikinta, bata taba sanin Nura ya iya waka hakaba, kuma saiya mata wakan hausa wanda yasan shine ta iya takuma ke ji, tana cikin kukan taga hannu dasauri ta dago jajayen idanunta Nura ne, ahankali yace “zaki rawa dani yar matata?” Gyadamai kai tayi da sauri tana murmushin kuka tasa hannunta yadagata shima ya mike aka kunna wani soft wakan hausan cikeda so yace “no more kuka” gyadamai kai tayi daidai an fara wakan yabi wakan yana nuna fuskanta yace “Kyakwawar fuska na kalla ta deben kewa Kuyi min san barka na samo fitilar 'yan mata” itama Ummi tana kallonshi daman ai ita oganniya ce awaka tace “Kyakwawar fuska na kalla ta deben kewa Kuyi min san barka na samo dan auta na maza” Nura nadan tafiya kadan kadan da ita dan bai iya rawa ba yace “Masoyiya” Ummi ta nunashi cikeda kware wa tace “masoyi na kai ne” yace “Aminiya,” tace “aboki na kai ne” yace “Ke zuciya” tanuna kirjinta kaman fa wata yar film tace “rabin raina kai ne” “Ke jijiya” tawani lumshe ido tace “jinin jikina” Yace “Kin zama komai na, abun kallo madubi na” Ummi tana wani reverse baya tana wani adorable kwarkwasa tana nunashi tace “Kai ne tinanina a barci na da mafarki na” Nura na murmushi dan yanda tayi ya mugun birgeshi yace “ban bari ki cutu, Zan zama garkuwa, Komai yake zuwa, Gareki zana tare shi” Ummi tazo yakama hannunta sukai juyi juyi chan yacigaba yace “Adadi na ruwan sama wanda suke zuba, Adadin kifaye ma ba a san su ba, Adadin bishiyoyi baza su kirgu ba, Haka soyayyarki a rai ban santa ba, Koda za'a au'na ba sikele wanda zai dauka Bata misaltuwa soyayya wace nake miki a zuciyata” Ummi tace “An san farkon rikici, ba a san karshen sa ba Soyayya gamu ciki, baku san haduwar mu ba Alkhairi ne a ciki, sam sam ba sharri ba,Karda ku ce, "Zaku raba, bazaka ku iya ba" yanda Ummi ke rawa sai kawai Nura yaciro kudi yana mata mani baitaba ganinta this happy ba, bakinshi yakai saitin kunnenta yace “kar rawan nan ya gajiyar min dake fa ban manta da wawatsulan nan ba”. 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣3️⃣ Magana ake ta kayan kwalam da makulashe😋 Kun gane kalan Kayan makulashe din kuwa? Toh bari kuji yau na kawo maki shaharariyar nan da aka sani da Crave and Indulge mai gullisuwan en gayu🌚 Indai magana ake ta gullisuwa, tuwon madara, tsami gaye, kwakumeti, Ridi, da halaka kobo,garin danwake da yaji! toh ba Irin ta a Nigeria. Zaku iya order ma kan ku, yaran ku, loved ones dinku har ma kuyi ma ‘yan uwa da abokan arziki souvenir😁 Ga tsafta ga dadi kuma✅ zaku iya tuntuban su a shafin su na instagrams @crave_n_indulge ko kuma ku musu magana ta WhatsApp https://wa.me/message/SAFXLSMA7TI6L1 33 Duk tafiya akayi yarage daga ita sai Mama afalon dake kallon yanda take kuka, kaman taje ta lallasheta but itama at this point she support Babanta 100 percent, yayi maganin Hadiza, ya gyarata, kuma she trust Baba Hadiza zata ladabtu, kuma zata bada nata gudunmawan ma agayarata, tashi tayi tawuce corridor dakin dake kusada nata tabude daganan tace “taho ki shiga dakinki kiyi wanka ki chanza kayan jikinki kiyi salla” ahankali Hadiza ta tashi ta taho sai kallon fuskan Mama take data hade giran sama da kasa so kawai take Mama ta lallasheta but Mama nosend hatta shige dakin dake da yar katifa yar daidai akasa dawata yar fanka asama babu AC babu POP normal silin ne asama, sai akwatinan kayan ta kakap wanda Nura ya aiko dasu duk suna dakin nan aka ijiye, shiga ciki tayi Mama tasaki labulen ta wuce taje ya debo mata abinci da ruwa da kanta tazo ta kawo dakin, ganinta azaune yasa ta daka mata tsawa. “My friend stand up kije kiyi wanka nace!” Kallon Mama Hadiza tayi saitaga kaman ba Mama dake nan nan da itaba, jiki asake ta tashi taje bayi tai wanka Mama na tsaye akanta ta shirya tai salla tasa taci abincin dole taci kusan rabin tuwon sanan tawuce tafita da plate din tadawo daki ta kwanta tayi shiru tana kallon fankan dake kadawa asama yana kara dake damun brain dinta sai kawai taji hawaye yafito daga idanunta saita tashi ta zauna ta zubama akwatinan ta ido tana kallonsu sai kawai taji hawaye yakara fito mata a fuzar da iska komi da Zeenah tamata na dawo mata fresh yanzu da gaske Nuri is done with her tunda har yana dawo da komi nata gida wani kuka yazo mata tayishi ta gode Allah tai bacci. 3 dot taji ana kiran sunanta. “Khadija Khadijah” Adan firgice tabude idanunta jin muryan Baba yana tsaye gaban dakin batare daya shigo cikiba yace “Khadija” dasauri tace “na’am Baba” strictly yace “dauro alwala kifito falo ina jiranki” ahankali tace “tom” tashi tayi tana tangadin bacci tashiga bandaki ta dauro alwala ta dauko hijabi tafito falo Baba kadai tagani ya tsareta da idanu dasauri tasauke kanta kasa dadduma biyu ya shimfida afalon daya agaba daya abaya yace “hau dadduma muyi qiyamun laili” Gyadama Baba kai tayi yatada salla yafara karanto Al qur’ani kira’an Baba dadi sai kawai Hadiza taji abun ya tsuma mata zuciya, yaune rana na farko dataji aranta lallai fa tabar Allah for a long time cus bazata iya tuna the last time ta karanta Al Qur’ani ba wlh, sai kawai taji hawaye ya gangaro mata feeling fragile, Baba bai wani ja sallan da tsayi ba sabida ita, 5 raka’a sukayi yajuyo ya kalleta anatse ya daga hannu yace “idan bawa na cikin kunci, damuwa da fitinun jarabawa, bawa dan uwansa bazai iya magance masa matsalolinsa ba Khadija, ni ko mahaifiyar ki bazamu iya magance miki duk abinda ke damunki ba Allah kadaine zai magance miki kome kikeji, shine Ubangiji mai tsarki da daukaka, mai kuma mulki, Al Awwalu, Al Akhiru Al Zahiru Al Badin kuma, duk daren duniya Allah kan sauko dakansa ya amsa bukatun bayinsa, dan haka daga hannunki sama ki gayama Allah bukatun ki kakap, sannan ki rokeshi gafara bisa laifuffukan dakikamai, ki rokeshi haske da dacewa akan rayuwa babu abinda yafi karfin Allah, so kaima Allah kukan ki Khadija” Gyadamai Baba kai Hadiza tayi kuka na zuwanmata ta hannunta sama ahankali abin namata kaman ba itaba she can’t remember the last time datai salla haka ta roki Allah for anything, she’s feeling guilty kan tayi neglecting bautama Allah, sai kawai tafashe da kuka tace “Allah na tuba! Allah na tuba!” Sai kuka hakan yasa ahankali Baba ya juya yayi facing gabanshi, Hadiza tai kuka zuciyanta ya sosu she’s feeling kaman ma she don’t deserve rahaman Allah cus tamai laifi da dama, da kyar ta iya controlling kukan tafara addu’a azuciyanta, the first abu daya fito daga zuciyanta is Nura tanson aurenta da Nura tanason ya maidata, tanason mijinta, kawai saita shiga share hawaye, sosai tai addu’a saitaji wani imani da natsuwa na shiganta da tadade bataji ba, anan bacci yayi gaba da ita ta kwanta kan dadduman Baba tajuyo yakalleta yayi shiru idan yace bai damu da damuwa ta ba yayi karya, saisa ya kudirci anniyan zai gyarata yana kuma rokon Allah ya taimakamai yabashi iko dan idan Allah bai nufeta da shirya ba kome zaiyi abanza bazata shiryu ba, addu’oi yacigaba dayı har aka kira asuba sannan yatadata yace “taje tayo alwala tai sallan asuba” shikuma yawuce mosque. Hadiza tadauka Baba wasa yake yana dawowa daga sallan asuba wanda bai dadeba dan normally sai gari yawaye yake dawowa gida but yau ana idar da salla yayi azkar yafito yadawo gida yakirata fitowa tayi ga mamaki ta ganin Baba tayi da bagadadi da gaske saikace yarinya shima Baba yasan duk tsiya ai ta iya alifun, ba’un, Al Qur’ani suka farayi from fathiha yana karantawa tana repeating after him, suna gamawa sukai alifun har karshe zuwa alifun bil fatha yana koya mata baki dalla dalla, daganan sukai tauhidi Man Rabbuka, Hadiza jitayi zatai kuka abu ya tsayamata awuya ganin yanda Baba ke koyarda ita abubuwan da yasan ta iya, ko su Aman dinta a islamiyyan su sun wuce abubuwan nan amman ya maidata yarinya, lekowa Mama tayi tagansu tadauke kai abinta takoma daki tana samin natsuwa ganin Baba yarike wuta. 7:30 suka gama Baba yace “tashi kije ki daura abincin kari kiyi gyaran gida, tambayo Mamanki me za’a dafa” gyadama Baba kai tayi tawuce ciki ahankali tace “Mama ina kwana” batare da Mama ta kalleta ba tace “lafiya lau” murya chan kasa tace “me za’a dafa Mama?” Dan kallonta Mama tayi tace “ki surfa wake rabin tiya, saiki debi kadan ayi kosai, ki dama kamu asha dashi, ragowan kiyi alalen rana na gwangwani, injin nikanmu na backyard banason alalen nikan blender, buhun gawayi na kitchen ki hura wuta” ahankali Hadiza na kallon Mama kirjinta na bugawa tace “ba gas Mama”? Wani kallo Mama tamata tace “akwai amman jiya Baban ki yasayo gawayi buhu daya yace dashi za’a dinga girki yanzu” hawaye Hadiza taji sunciko idanunta tarikesu dasauri tace “Mama ban iya hura gawayi ba, shima wake ban iya surfaw……” dakuwan da Mama tamata yasa takasa karasa maganan, Mama da haushinta ke cikinta fall sabida yanda takaso auren gidan arziki yaro mai kudi tadawo mata gida tawani zabura tace “wlh kikkipa miki mari zanyi Hadiza kinci kaniyanki, are you stupid dazaki cemin baki iya surfen wake ko iya hura gwayi ba kin dauka nan Abuja ne? Dan mai garinku kafin kiyi aure ba da itace kuke girki agidan nan ba lokacin akwai gas ne? Sau nawa kika dafa alale agidan nan ki surfa waken kiyi komi? Hadiza kalleni nan wake up! Ki gaggauta tashi daga baccin dakike ubanki ba kowa bane haka ma ni uwarki, Babanki Malamin makaranta ne nikuma housewife ahaka muka raineku kuka taso, auren Nura shine ya jiyardake dadin rayuwa kikadan menene rayuwa adukiya, yanzu kuma kin kaso auren gidan ubanki kike look at everywhere” Mama ta nuna dakin da yatsu tace “bude idanunki da kyau ki kalla nan ba gidan Nura bane gidan mahaifinki ne Hadiza, ki gane banbancin so my dear bace min daga nan kije ki daura abincin safe” tashi Hadiza tayi ahankali tawuce tafito idanunta har zafi zafi suke mata tsabagen rashin jin dadin rayuwanta, tsakar gidan tafito zuwa kitchen dinsu ta tasaya tana kallon komi ga buhun gawayi ga murhun gawayin, ga tukwane, yanzu itane zatai aiki a kitchen din nan? Tasan tayi aiki aciki da but ta manta? She’s not use to old life nata again, ijiyan zuciya tasauke tasa hannunta tadauki kaskon wutan ta ijiye waje daya, tabude buhun gawayin, tadaga fararen soft hannunta dakeshan manicure ta kalla, kuka tafashe da shi ahankali tace “na shiga uku na lalace” goge fuskanta tayi da sauri kafin ahankali tasa hannun cikin buhun ta debo gawayin ta zuba a murhun, ledojin datagani da kyallen dinki na hada kasko tadeba ta zuba tana mamakin yanda take tuna yanda ake hura wutan yanzu, bataga kalanzir ba saitadau ashana ta kunna akai makamashin suka kama hakan yasa tafito tawuce flat nasu ta auno wake 8 cup tafito tadeba ruwa ta jika tadauki turmi ta bude tadauki tabarya ta kwashe wajen ta zuba tafara daka ahankali kirjinta namata badadi ko kadan. Kafin kaceme hannunta sun sassage from surfen sakin tabaryan tayi ta zauna akasan simentin wajen jitake kaman zata sume ta jinginar da kanta a bango tana maida ijiyan zuciya tana yarfe hannunta, hayaki taga yana fitowa sosai daga kitchen din hakan yasa ta dafa bango da kyar ta mike tsaye ta wuce kitchen din, makamashin sun cinye gawayin bai kama ba sai hayaki suke, tari tafara sosai tafito daga kitchen din tawuce takoma daki tasami Mama afalo tana waya tace “Mama charcoal din yaki kamawa” batare da Mama tai magana ba dan waya take ta rarumi throw pillow kan kujera zata jefa mata da sauri Hadiza tafice takoma kitchen din ranta ba dadi. Mafici tadauka tashiga hurawa but still yaki kamawa fitowa tayi tawuce daki wajen Mama again data bita da kallo ganin tai buzu buzu duk toka toka akanta, ahankali Hadiza ganin Mama tagama wayan tace “Mama yaki kamawa wlh nayi nayi, gawayin baida kyau zoki duba dan Allah” wani matsiyacin kallo Mama tamata tace “Baban ki ya shigo gidan nan baki gama ba wlh zaki gamu dashi” juyawa Hadiza tayi takoma kitchen ta duka tasake deban makamashi tasa yagamaci still yaki kamawa kawai saita fashe da kuka she’s so fuatrated kaman taita zuba ihu takeji da kyar akaro na uku yakama tadaura tukunyan ruwa tafito tazo ta kwashe waken data surfa daga turmi taje gaban pampo tazo ta wanke da su attarugu da albasa taje chan backyard ta tsaya tana kallon injin din da ake mishi tadawan generator. She used the injin before dan su basakai nika waje but yanzu batasan tayaya zatayi ba, ijiye bowl na surfen waken tayi tazo gaban injin din ta tattaba, sannan takama handle na igiyan ijiyan zuciya tasauke sau uku na gathering strength kafin ta fuza da karfinta wani tangal tangal tayi zata fadi ta dafe bango injin din yayi kuka. “Tututututututuuuuuuu” ya mutu bai kunnu ba, sake zuwa Hadiza tayi tasake fizgan igiyan wanan karan saida ta fadi duwawunta ya bugi kasa tace “wayyooo Allah na” lekowa wajen Mama tayi ganinta akasa tsaki taja kafin taje tajima kanta ciwo bari ta tayata tada injin din just for today, ja daya Mama tayi injin din yatashi takalli Hadiza tace “tashi ki wanke injin din kiyi nikan” da kyar Hadiza ta tashi Mama tawuce kitchen din dan ganin haukan datake, ganin ta hura wutan harma ruwan na shirin tafasa yasa tai murmushi tawuce takoma daki. Da kyar tayi nikan ta kashe injin din takoma cikin gida, tana zuwa ruwan ya tafasa ta dama kamu tadaura mai awuta ta debi kullin kosai tana bugawa sai zufa take tasa gishiri da magi guda da albasa data yayyanka albasan shima saida yasata kuka sabida yaji, wlh zaku iya mata kuka kuka ganta a kitchen din nan, hannunta duk bakin gawayi harda fuska nan, tasoya kosen ta kwashe akula tafito daidai Baba da Baffa Amadu na shigowa har ranshi Baba yaji dadin yanda she manage tai girkin dan bai zacima zata iyaba that means yanada hope zata gyaru duk fitowa sukayi zasuyi kari zata tashi takoma kitchen Baba yace “ina zaki”? Ahankali tace “zanje nasa alalen a wuta ne” wuri ya nuna mata yace “zauna kiyi karin kumalo kema” zama tayi duk sukai kari ba laifi kosan yayi dadi wlh sosai, tafa iya girki dama kawai iskanci ne ke hanata yi, tass aka cinye ta kwashe komi tafito dashi takai pampo taje kitchen ta dauki buhun gwangwani tabude takai makawarara ta wanko tazo tahada tasa alalen ta zuzzuba a gwangwani ta jera a pot tasa a wuta sannan takoma tai wanke wanke tashiga share tsakar gidan tana gamawa tashigo falon su ta gyara har zuwa dakinta sai nishi take kaman mai asma, komawa kitchen tayi alalen ya nuna tadaura ruwan zafi dazatai wanka dan babu water heather agidan nan, ruwan na tafasa tajuye a bucket ta sirka ta tafi bayinta tadade aciki dan gashi tama jikinta lafiyayye tagaji, tafito tayi shafe shafenta tayi face routine nata ganin har tasoma samin wrinkles from this work datayi tasa kaya ta kwanta agado tana nishi barci kawai takeso tayi, harta runtse idanunta zatai bacci Mama ta kwala mata kira dasauri tabude idanunta daidai Mama na daga labulen dakin ta kalleta hannunta rikeda kayan wanki ta zudda akasa tace “kin wanke bayinka gidan”? Girgiza matakai Hadiza tayi Mama tace “ga kayan nan ki hada da naki da kika cire jiya dan ba’a tara wanki agidan nan kije ki wanke kiyi amfani da ruwan kumfan ki wanke bayukan gidan” duk yanda Hadiza taso tadaure saita kasa danta gaji ainun, fashewa tayyi da kuka tace “Mama harda ke baki sona ko yanzu? Mama kasheni zakuyi da aiki? Wlh bayana ciwo, hannuna har bororo yayi sabida surfen danayi kalli” tanunama Mama hannunta dahar yayi ja yayi bororo tace “Mama nagaji, Mama wlh nagaji” dudda ta bala’in bawa Mama tausayi amman ta daure tace “Dan girkin dakikayi na bakinmu kadai bawai girkin tukunya lamba goma ba, da dan sharan tsakar gida da wanke wanke da gyaran falon nan dakikayi shine kika gaji? Bayanki na ciwo? Surfen wake gwangwani takwas bama tiya daya ba shine hannunki har yayi bororo? Lallai Hadiza kin sami duniya, kinsan akwai matan da kullum aduniya sai sun surfa kayan hantsi buhu buhu sabida su sami abin ciyar da bakinsu abinci? Kinsan matan dake zuwa aikatun suna share big big organizations din nan irinsu bank da hospital sannan su wanke bayukan suyi komi sabida su sami kudin ciyarda kansu da iyalansu? Hadiza kinsan menene rayuwa kuwa? Sabida kin dandana dadi? Hadiza kinsan the amount of work people are doing in this life just to survive? Kinsan akwai wayanda yasan kashin damukeyi ne aikinsu? Kinsan akwai wayanda gyaran kwatane aikinsu? Kinsan akwai yan aikin kwadago? Kika har sunyi doro tsabagen aiki? You are complaining sabida kin share falo, kin dafa abinci? To ba ciwo baya ba, ke bayan ya karye ma kinji, tashi ki karasa aikin ki, jeki wanka bayikan gidan nan ki hada kayan nan ki wanke su tass you lazy girl, u might be 33 but mu muka haifeki you must work this work, da kinsan bakison aikin dabaki kaso auren ki kin dawo mana gida ba, da baku nan aini ke komi dakaina da tsufana banda yar aiki, yanzu ko kin kaso aure kin dawo gida ai Alhamdulillah nima nahuta, you don’t expect me to be entering kitchen gaki agida, kezaki komi Hadiza yanzu kika fara, bayan ya tsinke ma inyaga dama you will get use to it, tashi kona kira Babanki wlh ai yana wajennan” tashi Hadiza tayi kawai tafashe da kuka tace “na shiga uku” Mama tace “tukunna saikin yabawa aya zakinta Hadiza don’t think punishment ne wannan this is normal aikin gidan Babanki which You MUST DO” cikin kuka sosai Hadiza tace “Mama to nayi order washing machine da generator? Na yarda zan dinga wankin a washing machine, koba wuta saimu tada gen, Mama ni gas dinma zan iya sayo wani daban tunda bakuso ina girki da naku, please Mama dan Allah Mama basai Baba yasani ba kurufamin asiri Mama ki yarda wlh zanyi order yanzu nabiya kudi akawo” wani kallo Mama tamata ganin har yanzu da sauranta Mama tace “Hadiza dagani har Babanki are not interested in your money, kudinki is useless agidan nan, abinda Allah ya hore ma Babanki yasaya dashi zamuyi amfani, shikuma zamuci dan haka ko amarfi don’t even dream of zaki sayo wani abu ki kawo cikin gidan nan, karki bari nadawo nasameki zaune adakin nan”. Kuna ganin idan Baba da Mama suka gyara mana Khadijatul Kubrah bazatama Ummi fincikau ba kuwa🤣 Tundaga Alifun Ba’un fa aka fara mata. Akwai wani magana da manya keyi na cewa no matter inda kasami kanka arayuwa always remember where you are from 💔 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣4️⃣ Lokacin sabunta BUDURCI yayi…Lokacin sake HONEYMOON yayi…Lokacin dawo da martabar SOYAYYARKI da maigida yayi Shi lokacin AMARCI yafi ko wani lokaci dadi a rayuwar aure…shiyasa yau NASARA NERA ke gabatar muku da SABON package dinmu wato VIRGIN AGAIN VIRGIN AGAIN package ne na musamman ga duk wacce kaddara ta gifta ta rasa BUDIRCINTA Wannan package ya k’unshi 🔥Powder 🔥Steaming herbs 🔥Gel 🔥liquid Me kike jira??? idan ma aure zai k’ara kina da damar kasancewa daidai da amarya, idan kuma haihuwa kikayi zaki iya daidaita kanki kafin resumption, in kuma bazawara ce kin samu damar tashin kan ango🔥🔥 Me kuke jira??? Virgin Again wato sabon budurci munyi shi ne don min matan aure dage fama da matse war gaba ,kaman matan da suka haihu,ko kuma matan da Allah ya hada da kaddarar fyade. Bayan matsi da ya keyi yana maganin Infection. 07064487800 https://chat.whatsapp.com/IPh3BxIWPT6D9QsS49DkfB Our FLAT TUMMY PACKAGE is made with ingredients such as honey, sip and lipton and results is achieved within a maximum of 50days …Yes its no magic, not 5days …50days of FLAT TUMMY JOURNEY….would you like to join the flast tummy gang? Send us a DM NOW!!! 34 Bayan Wata Daya. Tafiya tai tafiya rayuwa taja, tunda Hadiza tazo gidan Baba wannan routine din nan Baba yake bitamata kullum yaumin, babu randa bazasuyi karatu ba, kowani abu kotanaso kobataso bata isa tace bazataci ba, zaman gidansu yasa taga life from a different angle cus Baba technically shows her kudinta is trash a inda yake dan bai mata amfanin komiba, at the same time itama tai regretting so many things, cus zata iya cewa business dinta da jikinta dasu Amali kawai take kashema kudin, chanza mota, siyoma yaranta designers outfit na yara she neglected gidansu, bawai sabida rowa tai neglecting ba but sabida taga Nuri namusu komi, sai yanzu data shigo gidan tai zaman gidan saitakeji inama ita ta buge gidan gabaki daya an chanza gini, ta zuba air conditions da sauransu dudda tasan ba lallai Baba ya yarda ba, then she remembered ko kafin Baba ya yarda da motan da Nuri yasayomai saida aka kai ruwa rana but dudda haka maybe da Baba yafi zama comfortable da cin kudinta than na mijinta and funny enough ko Mama or Baba basu taba rokonta wani abubu, so taga rayuwa outside abinda tayi and she must say she has not been a good daughter to them wlh nor a good mom to yaranta, abubuwa alot made her to reflect back and ask kanta what is wrong with me?? Inata rayuwane all this while kaman tinkiya, infact I have no right to blame Ummi sabida yarana na sonta wlh wlh nine nasa suka sota sama dani mahaifiyarsu gashi yau wata daya kodan kewanta basuyiba balle suce akirata suyi magana da ita,abun yadameta matuka. Ko kofar gida bataje ba tun bayan tashigo gidan nan ta iPad nata take monitor business nata da daddare dan bata samu ta zauna kota huta through out da rana, tunanin Nura da yaranta ya addabi zuciyanta takira Nura amman number shi baya shiga, WhatsApp taga yayi blocking nata, IG ma dan business page nashi na real estate business nashi a IG taje ta duba she can’t find d page shima yayi blocking, batada any means na ganin yaranta, kowa na gidan ya tauysaya mata but tasasu in a position da kowa kunyan kiran Nura yake sabida abinda ta aikata, but bala’in tausayinta suke barinma ranan data basu labarin abinda Zeenah tamata inda Mama tace yamata daidai it serves her right amman fa sun tausaya mata kuma ba Mama kadaiba hatta Baba duk suna mata addu’a kan Allah yasa Nura ya komar da ita kafin tagama Idda dan Nura mutum ne da kowa zaiyi sha’awan auren shi da diyarsa, gashi tana masifan kewan yaranta, for the first time in her life saitaji tai nadaman yanda yan uwan mijinta da mahaifiyarsu bata shiru dasu da nan nan ko Meena saita kira zata samu tai waya da yaranta abin ya taba mata rai sosai, ta wajigu kuma tagane ta tafka shirme karatun da Baba ke kara mata yakara samata tsoron Allah da tsantsan nadama aranta kullum sallan darenta saitayi addu’a kan Nura yakomar da ita dakinta, aurenta da rufin asirinta dan duk business da kudi is all trash idan ba namiji. Yauma kaman kullum ta tashi tayi duka abubuwan datakeyi ta daura ruwa awuta taji da kanta da cikinta na ciwo wanda tun jiya da daddare taji hakan amman datai bacci ta tashi bata karaji ba sai kuma yanzu datake kitchen din nan. Iza ruwan tayi tamike tsaye ahankali saitaji maranta ya rike sosai mamaki tayi period zatayi ne to ko shine ai bata ciwon mara haka, daurewa tayi tana dafa bango ta lallaba tafito daga kitchen din tana fitowa kaman ance oya kara tafiya mugani kawai kafanta ya rike tana ganin jiri d next thing kawai ta zube awajen daidai Baba da Amadu na shigowa gidan tana landing akasa akan idanunsu, Baba yace “Subhanallahi Khadija” da gudu yayi wajen ya tallabo kanta tana bude idanunta kadan kadan tana kallon su, Baba Amadu ne yafara ganin jinin dakebin kafanta dasauri yace “Yaya kalli” dasauri Baba yakalli kafanta yace “Subhanallahi, je tada mota” daidai Mama nafitowa jin hayaniya ganin Hadiza zube akasa ga jini a kafanta yasa dagudu tazo wajen hankalinta tashe abinku da uwa Baba yace “Hadiza nada ciki ne?” Arude Mama tace “ciki?! Ciki kuma, Wlh bantaba sani ba, ko miyar bata taba tofarwa ba, balle zazzabi ko amai, banganta ma da alaman mai ciki ba kwata kwata, bari na dauko hijabi” wucewa tayi aguje ta dauko hijabi akasa Hadiza amota Amadu yarufo gidan sai asibiti wani madaidaicin private asibiti Baba yakaita daidai kudinshi ba irin na yan gayun nan ba, karbanta akayi akai ciki chan Dr yafito ya nuna Amadu yace “kaine mijinta”? Dasauri ya kalli Baba yace “a’a lafiya meya faru”? Dasauri yace “ina mijinta yake?” Anatse Baba yace “likita meya sami diyata nine mahaifinta? Meya faru take bleeding”? Cikeda damuwa likita yace “Baba ko’ina mijinta yake just call him yazo maza maza, bari nakoma ciki, ya iso kwaji ko menene” yawuce yakoma ciki, Mama da hankalinta inyay dubu yatashi tace “kira Nuran Malam, Allah ubangiji yasa yana kano” dan Jim Baba yayi saiya wuce yafita waje yaciro number Nura yayi dialing. Cikin wani bacci mai shegen dadi sun gama watsewansu da Ummi yaji wayanshi na ringing hakan yasa da kyar ya iya yabude idanunshi, jaye Ummi yayi daga jikinshi ahankali yasa hannunshi yadauki wayan ganin Father Inlaw saida yayi dan jim har wayan ya katse bai dauka ba sannan yayi dialing number back cikeda girmamawa yace “Assalamu Alaykum Baba” dan ijiyan zuciya Baba yasauke yace “Nura ya gaji?” Ahankali Nura yace “Alhamdulillah Baba” anatse Baba yace “gamu a asibitin sangu yanzun nan muka shigo, kawai Hadiza ta sume gaban kitchen saiga jini ya balle mata” dasauri Nura ya yunkura ya tashi daga bakin gadon dayake zaune, anatse Baba yace “sunki gayamana komi Likita yace lallai lallai saina kira mijinta, ana nemanka saisa nakiraka dudda nasan kana Abuja maybe saina yasaka da Likitan awaya ko”? Anatse Nura yace “ina kano Baba gani nan zuwa” ahankali Baba yasauke ijiyan zuciya feeling calm jin yana kano yace “toh” ijiye wayan Nura yayi yakalli Ummi dake bacci dukowa yayi yaja bargo ya rufanata yana kallon kirjinta da kullum kara girma suke yarasa dalili maybe dan yana matsasu ne oho yawuce bayi wanka yayi yafito ya shirya cikin wata farra yadi mai kyau yana cikin fesa turare Ummi tabude idanu kallonta yayi yace “kin tashi baby girl”? Gyadamai kai tayi ahankali saka agogo yayi yazo bakin gadon ya duko ya manna mata kiss agoshi cikeda so yace “zan fita me zan kawo miki idan zan dawo”? Murmushi tamai tace “babu abinda yakaika dadi ni kadawo da wuri kada in kewanka, me zakaci na dafa maka?” Murmushi yayi cikeda so yace “yau nama nakeso naci but bansan ko Hajiya nada naman rago ba idan akwai kimin farfesu idan babu call me zan kira akawo” gyadamai kai tayi tace “saika dawo Allah karemin Baban Amali” “Ameen Maman Amali” yafadi yanajan hancinta ya mike tareda daukan wayanshi yafita dakin Hajiya yaje ya sanar da ita tace “imaxa kaje Allah yasa lafiya” ahankali yace “Ameen” yawuce tareda shiga mota yaja yasan hospital din hakan yasa yaje yayi parking ya sauka tareda wucewa ciki yana shiga yaga su Baba da Mama gaban wani daki hakan yasa yakara sa wajen cikeda girmamawa ya gaisa dasu akunyace yana kallon dakin daya hango Hadiza da likitoci akanta ta glass door din idanunta lumshe, tsayawa yayi yay jim yana kallonta, kusan 10min yayi awajen saiga likitan da nurses din sunfito ya kalli Nura yace “kaine mijinta”? Danjim kadan yayi kafin yace “yes” “come with me please” Dr yayi magana yana tafiya Nura yabi bayanshi zuwa office nashi suka zazzauna Dr yace “why was parent nata skeptical about calling you danake nemanka?” Dan shiru Nura yayi sai chan yace “bana tareda ita ne yanzu” kallonshi Dr yayi yace “dudda haka dai cus na tabbata cikin dake jikinta nakane” kallonshi Nura yayi dasauri, gyadamai kai Dr yayi yace “yes matan ka na dauke da cikin kimanin 2month da sati biyu but unfortunately……” yadanyi shiru kafin ahankali yace “yafita cikin tayi barinshi!” shiru Nura yayi kaman ruwa ya cinyeshi awajen, arayuwanshi yanason yara, shifa baiki yaga yanada 20kids ba wlh cus he just love kids, da kyar ya hadiye abinda yaji awuya har saida Dr yaga yanda Adam Apple dinshi yayi motsi, ahankali Nura yace “Dr are you sure Babyna yafita? Inace ba yanzun nan tafadi aka kawota ba kunyi scanning ne? Taya kuka tantance cikin yafita”? Yayi maganan cikeda damuwa, dan murmushi kadan Dr yayi ganin mutumin nada son yara from maganan shi dukya rude ya dimauce, dan ijiyan zuciya ya fuzar yace “that’s even the reason yasa nace a nemoka inaso kayi signing this document, tana bukatan wankin ciki cus cikin ya zuba but bai gama ficewa tatas ba” dasauri Nura yadagamai hannu yace “nooooo!” sai kawai ya mike tsaye dasauri jin yanada hope yace “just give me bill let’s pay zan maidata hospital na Abokina” yayi maganan yana kiran Dr Tanimu instantly, ringing daya yadaga yace “kana hospital? Zan kawo Hadiza yanzun nan” kawai ya katse wayan duk Dr na kallonshi yajuya yafita nan da nan duk su Baba na kallonshi yabiya kudin komi yataho dakin da Hadizan take shida wasu nurses suka daurata kan wheelchair duk she’s unconscious suka fito su Baba suka biyosu, wajen motanshi Nura yawuce dasu duk su Baba na kallonshi, da taimakonshi suka dagata daga kujeran sukasa abaya sai a lokacin yajuyo arude ya kallo Mama dake tsaye taredasu Baba yace “Mama zoki zauna da ita anan saisu Baba su biyomu” Toh Mama tafadi ta taho ta shiga su Baba suma suka shiga tasu sukabar asibitin, sosai Nura ke sharara gudu bini bini yana juyowa yana kallon Hadiza da Mama tadaura kanta kan lap dinta, nan da nan suka kai wani babban private hospital na masu kudi already Dr Tanimu ya shirya daki da komi aka karbi Hadiza kawai Nura yasami waje ya zauna yana bug buga kafanshi akasa looking so worried, he’s just praying Dr Tanimu zai fito yagayamai nothing happens to babyshi yana cikin tommy Maman shi alive and health, Mama da Baba duk tana kallon Nura suke kusan yamafisu iyayenta damuwa har ranta Mama take addu’a Allah ya daidaita Nura da Hadiza dan Nura care about Hadiza alot, jibi yanda duk yadamu, kusan 20min Dr Tanimu yadauka adakin yafito dasauri Nura yatashi ganinshi yabi shi zuwa office kasa zama ma yayi yace “tell me babu abinda yasami baby na pls”. There this connection tsakanin Nura da Hadiza i don’t know am i the only one seeing it ko kuma kuna gani??? Is this real love koko kawai affection ne as per anyi zaman tare da?? Hadiza Nura yakeso ko babyn shi dake cikinta??? 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣5️⃣ Wae har yanxu bakije shagon Habisma Underwears ba? Kode bakya Maiduguri ne? To shin kinje shafinta na Instagram ko TikTok? To yaude ki leqa Instagram, base kinyi following dinta ba, kawae kije Kisha kallo, in akwae wani abinda kike buqata Baki gani bama kitambayeta, wasu abubuwan basa samun dama suyi posting dinsu! @habisma_underwears. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=11rv83nzhagn6&utm_content=i5wy1kf *** Yau I need to get somethings off my chest. So a lot of people nata zagina, (M Shakur baki da hankali, me Hadiza tamiki kodai sunan kishiyanki Hadiza ne, akwai wata Hadiza data taba offending naki ne, the hate you have for Hadiza is too much, this writer don’t know what she’s doing, this writer is selfish, she’s bias, Haba abubuwa sunma Hadiza yawa bakida tausayine, wannan littafin baida ma’ana idan naji wasu zasu karanta ma zan hanasu, M Shakur I hate you) hmmm my people babu abinda ke bracket din nan da ba’a gayamin ba and more all because of this book MATAN KO MAZAN??? Now listen! If you can’t take this book kidena karantawa! Allah yasan ni banjinma family mu akwai me sunan Hadiza ba or wata Hadiza ta tabamin wani abuba, abubuwan nan dakuka gayamin all because I am trying to create awareness and still teach something on top of that kesa ake cema mata munada brain din KIFI! Are you even blind to think this book is about kishiya??? My dear this book is about feminism, are you too blind to see abinda nakeyi in this book?? Book din danai involving full circle na zamantakewa Mata, Miji, and Familyn su da iyayensu! Kun dauka inayin this book to downgrade first wife ko second wife ne?? Ask yourself Maisa nakawo Hajiya, Kannen Nura, Hadiza, Baba and yan uwan ta, Su Zeenah and co just ask kanki. I write this book to tell you what feminism is! To tell you how feminism are affecting our homes! To show you the implications of feminism! Abinda feminism kesa ki loosing, and to show you the end result of feminism, banda haka to show you how yan uwa, friends and family suma suke taka rawan gani in everything. I am hurt da all the insult but it’s okay! Allah knows best! Just remember one thing ko kina team Hadiza ko Ummi ko Nura your judgement doesn’t influence my writeup sakon danakeso na isar saina isar da shi! Idan bakiso ki karanta karkiyi as simple as that! 35 Shigowa office din Mama da Baba suma sukayi hankali adan tashe, cikeda damuwa jin har lokacin Dr Tanimu bai bashi amsa ba yace “tell me, did you save my baby”? Dr Tanimu na kallon Nura a natse ya girgizamai kai cike da damuwa ahankali Nura ya dafe kanshi tareda zama akan kujeran gaban table din dabas, Mama da Baba sukai salati, ahankali Dr na kallon Nura da har lokacin ya dafe kanshi yace “I am so sorry Nura, the thing is cikin yadan kwan biyu da lalacewa ajikinta kawaidai yau ne Allah ya kaddara zai fita, sorry Abokina, Allah yasa mai ceton kune” su Baba suka amsa Ameen, Nura yadade ahaka shi mutum ne mai tsananin son yara, he loves children, he loves children, dafashi Baba yayi yace “ya isa Nura Allah sa mai ceton ku ne” gently Nura yadago kanshi idanunshi sunyi ja ya kalli Baba tareda gyadamai kai, Baba yace “saika fito” shida Mama suka wuce suka fita, da kyar ya iya signing amata wankin cikin, yaciro wayanshi ya sanar da Hajiya, ita Hajiya ko kadan bataji dadi ba dan tanason jinin danta kodako daga jikin waye zai fito kuma tasan yanda Nura keson yara yawanci yana yawan gayamata yanaso Hadiza takara haihuwa amman ita tanason spacing yara so she really felt bad itama addu’a tamai suka katse wayan. Fitowa yayi daga office din da tuntuni Dr Tanimu yafito yabarshi shi kadai, wucewa yayi inda su Baba suke zazzaune a reception din, sai kuma yakasa zama yawuce hanyar dakin tiyata din dayagani an wuce da ita, yakasa tsaye yakasa zaune sai zagaye yake awajen, chan yaji ihun Hadiza wlh saida kanshi yasara dasauri yayi wajen dakin da aka shigar da ita wanda yake kusa da dakin tiyata room, wata Nurse yagani zata shiga ciki tace “Sir you are not allowed to be here” cikeda damuwa sosai Nura yana kallon kofan dakin yace “why is she screaming like that please? Ba amata alluran kashe zafi bane?” Ganin yanda yadamu Nurse din tace “Sir trust me ahankali ake mata nan da 10min angama baya daukan lokaci jeka zauna please” Gyadamata kai Nura yayi yawuce jin yakasa standing ihun sai kawai yawuce fuuu yafita. Duk su Mama da Baba na kallonshi chan saiga Anty Jams tashigo asibitin hankali tashe tawuce wajensu Mama. Nura na tsaye jingine da motanshi wayanshi yahau ringing daga wayan yayi ganin Baba ne yasa yamaida wayan aljihu yawuce ciki dasauri, Baba yagani yana kokarin fitowa yace “angama an fito da ita anma kaita dakinta idanunta biyu Alhamdulillah” Dan ijiyan zuciya Nura yasauke, suka wuce shida Baba ciki har zuwa dakinta, ahankali Baba yabude kofan Nura na biyeda shi abaya private room ne na mutum daya idanunshi kyur kan Hadiza da idanunta biyu sun kumbura sosai sunyi jaaa ga zufa agoshinta gashin idanunta sun tartare alamun tasha kuka tana kokarin kurban ruwan dumi da Anty Jams ke bata babu wanda yagaya mata Nura na asibitin but kawai kamshin turaren shi ne yadaki hancinta da sauri tajuyo da kanta ta kallo wajen kofan, hada idanu tayi da Nuran dake kallonta bayako kyafta idanu yana kokarin shigowa dakin biyeda Baba gabanta yawani kalan fadi ganinshi, dauke idanunshi yafara yi daga kallonta yatura kofan bayan yashigo ya rufe ya tsaya daga wajen Baba yakarasa gaban gadon ya kalli Hadiza dake kallon Nura takasa cire idanunta daga kanshi yace “sannu sannu kinji Khadija, yaya jikin?” Ahankali tace “Alhamdulillah Baba” Baba yace “meke miki ciwo yanzu”? Wajen maranta ta nuna tace “nan ne kawai amman kadan” hannunshi Baba yadaura awajen ya tofa mata addu’a yace “zai daina yanzun nan, bari naje nazo” yakalli Amadu kafin yakalli Nura yace “bari nadanje nazo Nura ai kana nan ko”? Gyadama Baba kai yayi, bawai Baba nada wajen zuwa bane kawai yanason yabasu space ne sun rasa dansu yanzun nan is only right suyi magana akai, Mama itama ta dauki nufin abinda Baba yayi ta kalli Jams tace “muje muhado mata shayin akawo wani riga ko Jamila” Anty Jams tace “to Mama” suka wuce suka fice dakin yarage daga Nura sai Hadiza dake kallonshi kaman yau tafara ganinshi yakara mata wani irin kyau a ido kaman tai shekara bata ganshi ba haka takeji, fatanshi yakara haske yanda kasan wani balarabe, she feels kaman yazo ya rungumeta and just talk to her kotaji dadi, bata tabajin ciwon rasa abu kaman yanda taji na cikin nan ba, da kyar cikin muryan mara lafiya dake a bala’in kwance sounding so weak tace “ina yini Baban Amali” dan kallonta Nura yayi kaman bazai karasa gaban gadonba saikuma yadaga kafa atsanake yakarasa gaban gadon ya tsaya tareda folding hannunshi a kirji yana kallonta kaman yanda take kallonshi heart dinta na racing kinship very close to her duka kamshin turarenshi na shiga hancinta, asanyaye akuma taushashe yace “are you having any pains?” Har cikin jijiyoyin dake zuciyanta taji tambayan dayasa zuciyanta yayi wani irin melting, girgizamai kai tayi ahankali, duk yanda take kokarin danne hawayen yakasa, she just wanna cry and cry and cry for him, she just wants to cry for her Nuri, hawaye ne masu bala’in dumi suka zubo daga idanunta takai hannunta da sauri tashare cikin wani kalan sanyin murya tace “I have no idea wlh inada ciki Nuri, nida from day one na sami ciki nake laulayi, but this is different banji komi ba, I lost our Baby Nuri, wlh koda wasa bansan inada ciki ba, I lost my baby, it’s hurts” tafashe da kuka sosai mai tsuma rai, he knows Hadiza so well she hardly tell lies, hakan yasa tana fadin batasan tanada ciki ba ya yarda without a doubt, cikin kuka sosai taga an miko mata handky hakan yasa tadago rinannun idanunta ta kalleshi hada idanu sukayi takasa tantance exact reaction dake kan fuskanshi but she’s happy yayi offering handkerchief nashi for her, hakan yasa tasa hannun ta ahankali tana kallon fuskanshi kaman bata taba ganinshi ba ta karba asanyaye tace “thank you” kai handkerchief din tayi kan fuskanta kamshin Nuri da warmth dake jikin handky din na jikinshi saitaji yakara tsumata tafashe da kuka sosai wanda yamafi nada, why will she make this coolest Man to hate her harya rabu da ita? Why did she pushed him to the wall, dan lumshe idanu Nura yayi yabude su ya daura akanta ahankali yace “stop crying please haka Allah ya kaddara, Allah yasa mai ceton mune, stop crying okay” yafada warming kaman yana lallashinta gyadamai kai Hadiza tayi ahankali tana goge fuskanta kukan yaki tsayamata she just wanna hug him, ahankali yace “bari naje naga Dr Tanimu” gyadamai kai tayi yajuya da sauri zai fice haryakai kofa tace “Nuri!” Tsayawa chak yayi batare daya juyoba dan lumshe idanu yayi ahankali yace “Nura dai” tsinkewa Hadiza taji zuciyanta yayi cikin murya dake dauke da tsananin shaukin so tace “I love you Nuri! I still very much do, I can never ever love anyone like you, Nuri forgiv…..” dasauri Nura yabude kofan yafice batare daya gamajin maganan ta ba Hadiza tafashe dawani kalan kuka kaman ranta zai fita. Office na Dr Tanimu yawuce, zama yayi Dr Tanimu yakalleshi yace “sorry about your Baby Nura” gyadamai kai Nura yayi yay shiruuuu sai chan ya fuzarda iska yadago idanunshi da suka danyi jaa ya kalleshi yace “is something else wrong with her ne”? Dasauri Dr Tanimu yace “nope kaga wani abune”? Dan lumshe idanu Nura yayi kaman baiso yayi magana sai chan ahankali yace “tayi duhu sosai, ta rame dik ta kode please kamata proper check up Dr Tanimu, she once had heart issue please kadubamin ita” ahankali Dr Tanimu yace “I think she’s stressed ne, stress din nema yaja mata barin nan, but dudda haka zan mata proper checkup idan yaso gobe sai ayi discharging nata daman anjima nake shirin nai discharging nata” gyadamai kai Nura yayi sai chan ya tashi yace “thanks” yawuce yafita, dakin yakoma yaga Mama da Jams aciki ga Hadizan bacci ya kwasheta tarike handky daya bata gamgam, tana sauke ijiyan zuciya ahankali, sallama yama su Mama yace zaidawo gobe duk sukamai godiya yawuce yafita daga dakin, daga Mama har Anty Jams babu wanda yaji dadin fitan cikin nan, hawaye Anty Jams ta share dataji ya zubomata da sauri Mama ta bubbuga kafadanta tace “is okay Allah yasan dalilin dayasa hakan tafaru, idan sunada rabon sakeyin zaman mata da miji zasuyi, so don’t worry and don’t loose hope dudda aure yakare tsakaninsu” gyadama Mama kai Anty Jams tayi takai duka hannayenta kan fuskanta ta share hawayen, tanason Nura da Hadiza dan dukansu sunason juna, but a yanzu Allah kadai yasan idan zasu cigaba da zamma taren, Hadiza tama Nura abinda take ganin kaman Nura yariga ya hakura da ita for good, Allah dai shine masanin komi. *** Washe gari Nura da kanshi yasa Ummi ta shirya su Amali zai kaisu wajen Maman su, murmushi Ummi tayi tace “Anty tazo kano itama yayyy, Aman yau zakuje wajen Momy” tai maganan tana wasa da yaran tana shiryasu Nura yayi murmushi kawai yawuce ciki dan shiryawa, koda yafito yaga ta shirya yaran sunyi kyau sosai kaman zasuje wani event, tasama Amali hair band akai, hancin Ummin yasa yana murmushi yace “sannu da aiki Anty Ummi” murmushi tamai tana juya idanu tace “saikun dawo agaida Anty, bye Aman da Amali” yaran sukai waving nata “bye Anty Ummi”Nura yaduko tareda mata peck a goshi yace “I love you” akunyace tarufe fuskanta tace “ka gaida Anty” kumamunta ya shafa yace “kunyan gulma kinfi kowa…..” tashi tayi da gudu tawuce uwardaka yayi dariya tareda girgiza kai yawuce yafita daga dakin, sallama sukama Hajiya suka fito kaga yanda yake hira da yaran kai kanka you will wish ka sami Baba mai son yara haka. Supermarket yakaisu yace “kuma Mommy ku shopping” yaran were so happy kowannen su ya debama Mummy abun da ransu keso, sukaje kanta yabiya kowanne ya karbi ledanshi na Amali yafi karfinta ya amsa yace “lazy Princesses” kaman zatai kuka tace “Dady I am stronger than owlett din pj mask fa ko Ya Aman”? Aman yace “yes Dady, nikuma I have lots of super power, Dady I can lift this car up” Dan zaro idanu Nura yayi yace “sannu special boy” Amali ta kwashe da dariya, Aman yace “Daddy kaga Amali ko Lazy princess kawai” wani tsalle Amali tayi zata fara halin dasauri Nura ya dauketa yace “yakuri Hajjaju, muje mu shiga mota” baya yabude ya ijiye Amali da kayansu shikuma su Aman first born adole babba ya shiga gaba yace “Dady I want to start driving nima” dasauri Nura yakalleshi duka duka fa Aman is just 4, kawai dai irin brilliant smart kiddo din nan ne sai kawai yayi dariya cikeda sonshi yace “okay Son zan koyama idan kakai 15yrs” tada motan yayi suka tafi sai hospital. Kashe motan yayi yafito Aman yace “Dady this is a hospital is my Momy sick”? Gyadamusu kai yayi yace “but taji sauki, muna zuwa zamu tafi mu kaita gida ma” gyadamai kai yaran sukayi ya rufe motan holding shopping din Amali suka wuce ciki sai kallon yaran ake dan Amali and Aman are so cute wlh kaman yaran larabawa, ga Ummi tamusu gayu, Aman kuma harda saka sun shade black na Rayban da Dadyn shi yasiyamai shi adole babba, dan baiso ana referring nashi as yaro. Ahankali Nura yayi knocking tareda bude kofan dakin, Hadiza na zaune kan gado Mama na hada mata shayi zata sha aka bude bude kofan kawai taga yaranta sunci gayu kaman ba su ba, looking finer and healthier than yanda ta barsu, dawani kalan gudu suka taho barinma Amali tace “Mommyyyyyyy” wani kalan tsalle Amali tayi Hadiza ta sauka daga gadon da sauri tadauketa sama Aman shima yazo yana cire glasses nashi, tsugunnawa Hadiza tayi tana kallonshi she can’t believe ita ta haifi this big handsome smart adorable boy, rungumeshi tayi sosai tana rike da Amal, kuka taji yazo mata but saita daure sabida su, bata taba tunanin Nura zai kawo mata su ba, she can’t even kwatanta excitement nata sai kawai tashiga mammanna musu kiss kaman zata hadiye su, Nura ya gaida Mama tabashi plastic chair ya zauna yana kallonsu kasa kasa. Shafa fuskan Maman shi Aman yayi yana kallonta dan yaron akwai wayau he understand a lot of things batare da an fadamai ba yace “Mommy what’s wrong with you? You look so skinny and dark” dasauri Amali tace “yes Mommy, meke miki ciwo? Ya Aman mu mata addu’a kaman yanda Anty Ummi ke mana ko”? Dan murmushi kadan Hadiza tayi tace “Momy’s tummy hurts” kaman zasuyi kuka sukace “sorry Mommy” Amal ta shiga tofamata addu’a Mama tace “wannan tsohuwan yarinyar da wayau” dan murmushi kadan Nura yayi, saida tagama ma Mommy addu’a, Aman yabata ledan hannunshi yace “Mommy I got this for you get well soon” kallon Aman Hadiza tayi yanada wani kalan charismatic composure na Baban shi, she can’t believe yaronta ne Aman, Alhamdulillah! Hannu tasa ahankali ta amshi ledan zatai magana itama Amali ta sauka da gudu ta dauko nata ledan dake gaban Dady akasa ta dawo da gudu takawo mata tace “Mommy I got this for you, get well soooooon Mommyyyy naaaaa” Amali tai maganan like a little sweet girl, bude ledan Hadiza tayi trying so hard ta rike kukan datakeji, ledan Aman tafara budewa drinks ya kwaso mata cres, yasan Maman shi na yawanshan, da vita milk da cake loaf, da peanut da biscuits manya manya Oreos da chocolate cookies, tabude ledan Amali kuma su minti mai tsinke da cingum ne aledan dayawa exactly shopping din yara dai, sai kawai tafashe da kuka ta rungumesu Aman yace “stop crying Mom is the tummy still hurting Dady call Dr for Mom” girgiza musu kai tayi tace “am just so happy ne yarana sun kawomin tsaraba, yarana are all grown up kunyi kyau, and I miss u very well” Amali tace “Mommy give me one sweet” dariya Mama tayi Nura ma yayi murmushi kadan Mama tace “kin kawo tsaraba kuma kina roka, kanki kika sayomawa kenan su Amali manya” murmushi Hadiza tayi tadauki sweet tabata takalli Aman daketa kallonta shima yana lurada duk yanda Maman shi ta chanza kaman ba itaba tace “mekake so kai ma nabaka?” Ahankali yana kallonta da this affection na mother and son yace “chocolate Mommy” wani kalan son Aman Hadiza taji ya shiga ranta barinma dayace mommy, dauka Hadiza tayi tace “nabude maka?” Gyadamata kai yayi yana kallonta har lokacin, tabudemai ta bashi amsa yayi yace “thank you” vita milk daya kawo mata tadauka tabama Mama tace “Mama budemin nasha” dasauri Aman ya karba yace “Dady will open it, grandma batada hakori” yaje gaban Nura yabashi, ahankali Nura yasa hannu ya karba yakai bakinshi ya bude dan ba opener adakin yaba Aman, Hadiza ahankali tace “thank you Dadyn Aman” zama duk yaran sukai kan gado kusada ita Amali nashan sweet, Aman na cin chocholate, Hadiza na shan vita milk tana nan nan da yaran, ahankali Nura yamike yakalli Mama yace “bari naga Dr nazo” Mama tace “to” fita yayi yaci karo dasu Baba akofa suka gaisa nan da nan yayi clearing all the bill yakarbo magungunan da aka bata yabiya yayi signing discargw papers din yataho dakin yabama Mama magungunan ta yace “an sallamemu mutafi” Motan Nura Hadiza tashiga da yaran da suka zauna baya da ita sai surutu suke mata su Mama kuma suka shiga motan Baba, suka tafi gidansu Hadiza parking yayi duk aka shishiga gidan. 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣6️⃣ Huuuuhuuuuuu agyara hanya gafa MAMMI HAJIA tazo mana da kayan mata wey no be juju, ba jazz, ba abacadabara ko suddabaru aciki amma kuma aikinshi yafi yankan wuka, MAMMI HAJIA fa tariga tayi suna awannan harkan dan haka ku garzaya aguje kar ayi baku zaku iya shiga whatsapp group nata ta hanyar danna link din nan. https://chat.whatsapp.com/L9xdTKd3MXZJRW8zkAMSqH 36 NOTE: akwai school of thought daban daban i read something daban daban kan idda. Ance bari terminate idda, at the same time some sunce sai cikin yazama mutum shine yake terminating idda Soo Allahu A’alam Allah masani, feel free to correct me or shed more light on the issue Allah ya ganarda mu gabaki daya Ameen. Yadan jima kadan amota kafin ya sauko, Baba Amadu ne yakaishi wani special babban falo na Baba wanda yawanci littafai ne na addini suka cikashi ga blue rug ya rufe ko’ina akasan dakin, zama Nura yayi ahankali kanshi akasa ganin Baba shima akasan yayi filo da wata babban filo haka, shigowa Anty Jams dakin tayi takawo ruwa a tray da cincin da soyayyen naman kaza saikuma kunun aya mai sanyi tawuce tafita, Baba yakalli Nura yace “Bismillah Nura” cikeda girmamawa yadauki ruwa yabude ya tsayaya a cup yakai baki yasha kadan Baba yayi gyaran murya yace “Nura” ahankali Nura yadago kanshi yakalli Baba, Baba yace “dudda nasan kasani but still zan gayamaka dakaina miscarriage din da Hadiza tayi yabata iddan ta! Auren dake tsakaninku yakare!” Baba yayi shiru Nura yasauke kanshi kasa ahankali Baba yace “banbancin ku da wacce akama saki uku shine ita dole saitayi wani aure kafin tasake iya auren mijinta while a case dinku koda yanzu kakeson auren Hadiza sadaki kawai zaka biya a daura muku aure” Baba yayi shiru yana kallon Nura da kanshi ke kasa yace “don’t get me wrong Nura, dakai da Hadiza duka yarana ne, sake aurenta ko rashin yin hakan bazai taba chanza matsayinka awajena ba and everything is your decision to make Nura kai d’ana ne, har yau har gobe har kuma jibi, sannan dagani har Amadu munsan abinda Hadiza ta aikata dan mu mazane dan haka live your life according to your rules and regulation Nura” gyadama Baba kai yayi ahankali nan Baba yakawo wani hira daban dan he don’t wanna make him be uncomfortable idan yanason ya maida Hadiza dakanshi zai furta basai ancemai yafadi ba Nura ba yaro bane yasan har cikin ranshi abinda yakeso kenan amman kuma baida right na nuna hakan. Azahar sukeje sukayi suka dawo gidan Nura zai wuce Mama tace “ai baka isa ba saikaci abinci koma” ba yanda ya iya komawa yayi shinkafa akayi da stew kadan yaci shima dan kada suce yakici sannan yatashi yama su Baba sallama, Mama tace “ka shigo ciki” shiga falon yayi Hadiza na zaune kan kujera tana sanye dawani doguwan rigan atamla red daya mata bala’in kyau hada idanu sukayi dasauri Nura yadauke kai yace “Allah kara sauki Hadiza” yakalli su Amali yace “let’s go kids” dasauri yaran sukai wajen shi suka kakkama hannunshi Aman na karban car key dake hannunshi, bawai basason maman su bane but wannan shakuwan dazaisa yaro yahau kuka shi zaibi Mamanshi ko zai zauna da Mamanshi daga Aman har Amali basu dashi, Amali da tayi but tazo tadaina dataga Mamanta no send her, hawaye Hadiza taji ya cicciko idanunta ahankali tace “Dadyn Amal bazaka barsu su kwana ba anan”? Still Nura yaki kallonta yace “maybe saidai gobe basuzo da kayaba” ga mamakinshi kaman ba Hadiza ba tace “Tom shikenan nagode Allah saka da alkhairi, nagode da komi da komi dakamin a asibiti Allah baka lada” dan dago kanshi Nura yayi just to assure kanshi Hadiza ne just agreed da maganan dayayi tashi daya hardamai godiya ganin itane dai yasa gently yace “u welcome” yama su Mama sallama suka fice su Baba suna rakasu har waje suka shiga mota Baba yadawo cikin gidan. Da sauri Mama cikeda damuwa irin na mahaifiya tace “Malam ya nuna zai komarda ita?” Daga Baba har Amadu girgizama Mama Kai sukayi hakan yasa ahankali Mama tajuya takoma falo kawai ta sami waje ta zauna tai tagumi dasauri Anty Jams tazo kusada ita tace “Mama menene? Yace zai komar da ita”? Itama Hadizan dake zaune kan kujera tana kallon Mama jira kawai take taji ance yace zai kara aurenta dan Nura nada tausayi, shigowa dakin Baba yayi yakalli Hadizan data bishi da kallo tana zazzaro idanu kana iya ganin yanda gabanta ke faduwa zama Baba yayi ahankali kusada Mama ahankali yace “iddan ki yakare Hadiza!” Yadanyi shiru anatse yace “bazan hanaki yin kasuwancin ki ba amman dai ki kira wayanda zaki kira akwaso kayayyakin shagon adawo dasu kano kina karkashina bazan bari kına tafiye tafiye ko ki koma wani gari dazama ba, zaki iya samin wani shago anan kano akama ki cigaba da kasuwancin har zuwa lokacin da Allah yafito miki da wani mijin dan Nura kwata kwata baiyi maganan sake zama dakeba” yanda Hadiza ke kallon Baba wlh wlh zaka iya zubar mata da hawaye kanta ta nuna lips dinta narawa sosai tanaso tama foto da magana ne but takasa sai kawai tafashe da kuka wanda yafi na ko yaushe cikin kukan tace “Baba a ina zan taba samin miji kaman Nura aduniyan nan?” Cikin tsananin kuka tace “A ina zan taba samin miji kaman Nura aduniyan nan” cikin kuka sosai tana girgiza kai tace “bazan taba samun miji kaman Nura ba aduniya! A ina zan sami miji in this my age 33 dazan shiga as first wife, ko ya yarda zai aureni wani iyaye zasubar saurayin dansu ya auro bazawara mai yara biyu as first wife nashi? Mama Kozan sami miji is either me mata biyu ko uku, I can never get mijin dazamu shimfida foundation na rayuwan aure together like Nura” tayi maganan tana zubewa kasan dakin dumus akasa tana kuka, daga Baba har Mama data buga tagumi kallonta suke kaman TV, Anty Jams kuma kawai tasanya hannu ta rufe fuskanta tana kuka kasa kasa. Hannuwanta biyu tadaura akanta tana wani kalan kuka tace “Anty Jams and Mama maisa dakuka ganni ina tsinannen akidan feminism din nan bakudau bulala kunmin shegen duka ba, ko kubani factory reset mari dazai dawo dani hayyacina ba, ko ki kira Baba ku fadamai? I was lost a lokacin all I needed was someone strict with irons hands that will put me in my place look at me today my life is messed up Baba yarana” tanuna kofa sannan takai hannunta tadaura saman cikinta tana kallon cikin tace “Baba yaran dana daukesu acikin cikin nan na haifosu duniya basuda emotional connection to me and is all my fault, look at them yanzun nan babansu yana cewa su tafi babu ko musu, ai sunaso su zauna da Mommy basuyiba sun bishi sun tafi because basuda emotional bond dani what kind of a woman am I”? Tafashe da wani kalan kuka harda majina dayasa Mama tafashe da kukan datake rikewa acikinta sosai idanun Amadu ma sunyi jazur Hadiza tabashi tausayi Baba ne idanunshi kyam akanta cikin kuka tace “I used to believe yara damuwa ne! I used to believe providing abinda yara keso shine love not knowing spending quality time dasu, playing with them hugging them and kissing them is real love, my children never miss me but they miss Ummi sabida she’s always with them, ta goyasu yarinyar nan ta goya Amali har nakan mata fada tana batamin yarinya da goyo har Aman Ummi goyawa take, I remember wata rana idan nadawo da wuri banson damuwansu nace ta kwashesu suje garden suyi ball that’s how zata dinga wasa da yaran nan while I provide the ball and other accessories for playground dinsu Ummi is the one dake wasan dasu, Baba na cuci kaina dayawa” tafashe da kuka tace “Nura is my entire life, Nura yabani freedom, yabani opportunity, yabani luxury, yabani love, Baba bazan maka karyaba i know all abubuwan danama bawan Allah nan was wrong but Baba kasan mesa nayi hakan? Yau zan fadamaka gaskiyan daban taba gayama kowaba” Tayi dan shiru tace “Baba all abubuwan danama Nura nayi ne sabida nasan yana sona and he will always tolerate me ya hadiye kome namai, ina ganin cewa kalan son dayakemin bazai taba iya rabuwa dani ba, so I can match him, step on him however and whenever I want kuma bazaimin komiba, I feel I can use him to please my friends, the community and association din damuke ciki ashe hauka nayi Baba ko wayanda nake biyemawa su Zeena bahaka sukema mazajensu ba bakin ciki ne sunga yanda Nuri ke sona saisa sukaci nasaran rabani dashi, nama Hajiya all abubuwan nan babu ko darr araina sabida nasan yana sona, kuma na isa dashi, nabiyewa Zeenah nakaishi kotu sabida nasan yanasona he can not do anything, barinma yanda yasan nasami heart attack, Baba wlh wlh Nura baitabamin komiba, mutum neshi dakeson farinciki na da cigaba na, mutum ne daya tsani ina fushi koya ganni cikin damuwa, Nura can kill for me and die for me, kuna ganin zan taba samin selfless miji like Nura? Zan taba samin mijin da duk kudina bazai kalla ba he will still give me kudin salon, kudin kaya, kudin dinki kudin komi? Duk kudina bai taba cewa muyi sharing bill ba, duk kudina bai hanashi kara bani kyauta an ina zan sami kalan mijin nan”? Tayi maganan tana kuka tace “I tortured Nura, I pushed him har ya zamto gwara yadawo gidan by 1 nadare Ina bacci, Baba I took advantage of that man, took advantage of soyayyan dayakemin, Baba na zageshi is not a big deal for me sabida nasan bazai iyamin komiba yana sona, munafuki, algungumi, makiri, matsiyaci, mahaukaci, and so much more babu wanda ban kira Nura dashi ba Baba, Baba nashiga uku wlh nashigo uku Baba, nazo nakaishi kotu Zeenah ta kara da accusing nashi for molesting me, namai shairi na batamai suna i spoilt his record, Baba koni nasan after komi danayi ban chanchanci Nura ya maidani ba amman kuma wlh wlh bazan iya rayuwa babu shi ba, Baba kaga kashin jikina, bargo, jijiya, jini dakuma tsoka na jikina duka Nura sukeso hatta numfashin danake busawa nake shaka Nura yakeso, Baba tell me how can I live without him? Nura is the world best husband that knows how to pamper and spoils his woman but I ruined him, I fucked up, I messed him up and tarnish his image because of stupid feminism mentality na we are equal nidashi, Baba wlh wlh Baba zaku rasani har lahira idan Nura bai komardani ba, Baba tsoron alhaki bazaima barni nayi wani aure ba dan kowa zan aura nasan sai Allah yasa ya gallazamini azaba wacce tafi wanda nabawa Nuri na sau dubu, Baba kaji tausayina cikin nan was the hope na zai komardani cus Nuri loves children but shima yafita, kai kadaine mahaifina hope dina Baba cus Nura najin maganan ka, yanajin kunyanka, kace ya aureni Baba, zuciyata zara tarwatse na rasa Nuri na, wayyooo Allah na ni Hadiza! Wayyyoo zuciyata na shiga uku, na bani, na lalace, na tagaiyare na ga ukuba, Baba dan kaunar dakakema Annabi Muhammadu SAW kasa Nura ya maidani” Tafashe da kuka majina shabe shabe for the first time Baba yasauke kai daga kallonta shima idanunshi sunyi jaaa but baiyi kukaba amman kowa na dakin harda Amadu tasa kuka. Kuna ganin Baba yama Nura magana??? But then again! I feel bad and emotional for Hadiza, for ita da kanta ta zauna tai analysis na laifukanta haka dudda ance hali zanen dutse but ina ganin mu jira Muga new Hadiza ne ko Yaya?? Kuna ganin ta chanza ko a’a??? 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣7️⃣ CHAPTER ONE IS COMING TO AN END😫 Labarin Nura da Hadiza yasoma karewa have you subscribe for chapter two?? Is just 1k, zamuyi magana akan Matan aure da Mazan aure masu biye biye, no judgement but I will teach you something you never knew about cheating and I will help you overcome it. Kome kikeyi don’t miss this chapter 2!! Chat me up today and make payment. wa.me/+2347012181461 37 Juyoda kanshi Baba yayi a tsanake ya kalleta dudda ta bashi tausayi but ya danne, yakalli Mama yanda take kuka da Anty Jams dama Amadu ya nuna Hadiza yace “duk sabida yarinyar nan kuke kuka?” Saikuma yayi shiru dan yanda Hadiza tafadi abubuwan datayi da bakinta sai zuciyan Baba yasake sosuwa ya nuna Hadiza up and down da hannu yace “kin dauka wannan borin da hayagagan nan dakikeyi shine zaisa nakira Nura namai magana?” Baba yadanyi murmushi mai ciwo yace “Hadiza yanzu haka ki fadi awajen nan ki mutu ni nasan cewa lokacin ki ne yayi bawai damuwan Nura ko wani abu bane yakasheki ba, cuta ba shine mutuwa, shi mutuwa lokaci ne kinsan mutane nawa har wankan gawa aka musu daga baya suka farfado why? Because lokacinsu baiyiba, idan lokacin mu yayi, ko yanzu, ko anjima, ko gobe, ko jibi ko gata, ko citta ko badin badadan zamu mutu Hadiza” yanuna kanshi da hannu yace “kin ganni nan dattijon arziki ne sabida ke bazan zubar da kimata a idanun Nura ba, bazan taba mishi magana yakomar dake dakinki ba idan yanaso yayi yayi idan bayaso duka daya awajena abu daya zan fada miki ki kama Allah ki rike addu’a kuma, sannan ki nemi gafarar wayanda kuka kuntata mawa Allah yasa mudace tashi Amadu muje” tashi Adamu yayi suka fice Hadiza tai kuka tai kuka har saida Mama tai ihu tace “wai bazakima mutane shiru ba kashe kanki zakiyi da kuka, kima mutane shiru dalla” tashi Anty Jams tayi tawuce inda Hadiza take kama hannunta tayi tadagata tace “muje daki” da kyar Hadiza ta iya tabi Anty Jams daki. Sunyi nisa sosai, Nura yana tuki yana kallon hanya ahankali Aman dake gefenshi yana kallonshi yace “Dady” dan juyowa Nura yayi yakalli yaron yace “yes Son menene?” Dan shiru Aman yayi sai chan yace “you don’t want to make Mommy come back home with us”? Dan kallon yaron Nura yayi sometimes tambayoyin Aman nabashi mamaki kaman wani babba, dan shiru yayi baice komiba ahankali Aman yace “Dady is it because Momy na zaginka”? Dasauri Nura ya kalli yaron kafin yace wani abu Amal ta taso da gudu tana leko da kanta ta wajen takalli Aman tana zaro idanu kaman wacce zatai gulma cikin whispering but kana iyajinta sarai tace “Ya Aman Momy use to call Dady munafuki…….” “Amal!” Nura yakira sunanta da tsawa saida yarinyar ta firgice tace “Dady sorryy ai bantaba fadi ba ko Ya Aman”? Gangarawa Nura yayi yay parking motan gefen hanya, yasan yaran sunsan suna fada but baitaba sani har zagin sun sani ba, dasauri yajuyo yakalli Amali daduk ta rude strictly yace “kika kara fadin something like this I will be very angry with you kinason Dadyn ki yayi fushi dake?” Girgiza mai kai tayi tafashe da kuka tace “Dady sorry” dan shiru yayi yana kallon yanda take kuka saikuma yace “come here” dasauri tazo hannunshi yasa ya share mata fuska yace “stop crying okay babu kyau yana suna sauraron fadan Momy and Dady is a bad habit” gyadamai kai tayi tace “sorry Dady” peck yamata a goshi yakalli Aman dake kallonshi yace “I dont want this discussion ever again am I clear”? Gyadamai kai yaron yayi yace “yes Dady” zaunar da Amali yayi, yatada motan tareda dan sauke ijiyan zuciya yawuce. Ummi na zaune dakin Hajiya tana matsa mata kafa basu dade da dawowa daga kesson ba itada Meena taga yaran sun shigo da gudu abin ya bala’in bata mamaki da Nura yayi sallama yashigo falon sai mamakin ya idasa kasheta batasa ran ganinshi ba yau danta dauka awajen Anty zai kwana yau, gaisawa yayi da Hajiya Ummi ta kalleshi akunyace sabida Hajiya dake wajen tace “sannu da zuwa Baban Amali” dan kallonta yayi yasakin mata good smile yace “me kika dafamin am hungry?” Tashi tayi tawuce kitchen din Hajiya, Hajiya dake kallonshi tace “yamai jikin?” Ahankali yace “dasauki gobe zansa driver ki yakaisu suje su kwana jibi su dawo, gata dasafe zamu wuce Abuja dukanmu” gyadamaikai Hajiya tayi tace “Allah kaimu, shima yaron nan dake neman auren Meena ai katuna gobe zaizo yaganka ko”? Anatse yace “natuna Hajiya Allah kaimu” abinci Ummi takawomai yaci yayi damm sannan yawuce masallaci bai dawo gidanba sai around 9, dakin Hajiya yawuce yamata saida safe sannan yawuce side dinshi Ummi na zaune tana duba wasu books yashigo da sauri tasaki books din ta tashi dagudu tai wajenshi murmushi yayi yace “ammata na” ahankali tace “an samari na” murmushi yayi yadagata suka wuce kujera suka zube lamo tayi ajikinshi ahankali tace “na dauka awajen Anty zaka kwana”? Remote yadauka yashiga kunna tv irin wanda bayason maganan nan yace “anan zan kwana” lurada yanayinshi datayi yasa bata kara cewa komiba daura idanunshi yayi cikin nata yace “kallon fa wawatsula kikeso?” Wani irin murmushi Ummi tayi tun ranan data gayamai kalman yarike gam yake fadi, kannemai idanu tayi tana lashe baki ahankali tace “ni gwaguyanka nakeso nayi” ohhh shi baimasan yanda zai misalta abinba but kobaiso dazaran Ummi tamai batsa sai jikinshi yatashi bakinta ya shafa idanunshi na kankancewa yace “menene kuma gwaguya baby” sauka tayi daga kan jikinshi takai hannunta kan idanunshi tace “rufe idanunka kagani” kulle idanunshi yayi kawai tai kneeling agabanshi tasa hannunta ta daga riganshi sama tana kwance mazariyan wandon yadin jikinshi hmmmmm… Saida Ummi takusan sakashi sakin mata fitsari abaki anan falo suka watsewan su. ** Washe gari around 11 nasafe Nura yasa driver Hajiya yakai yaran gidansu Hadiza. Jibin daya fadi jibin akaje daukosu suka dawo da tsaraba sosai washe gari suka wuce Abuja. Ummi kusan mutuwan tsaye tayi ganin durmemen gidan dasuka koma manya manyan flat daban daban guda uku ne komi iri daya, saida yafara shiga da ita ko’ina sannan yakaita second flat din inda yazuba mata furnitures naban mamaki a akwati saiti 16 jere a tsakiyan babban falon sai kawai Ummi tahau kuka dasauri yaran sukahau tambayanta menene shima Nura ma haka dago rinanun idanunta tayi takalleshi tace “ko amafarki bantaba tunanin zanyi rayuwa a irin wannan gidanba, kamin komi kuma, ga akwatina kaman wata yar sarki” murmushi yamata yace “kına kuka agaban su Amali, Amalili look at Anty Ummi is crying let’s make her smile” sai kawai yama Ummi chakulkuli suma yaran sukahau mata tahau dariya sosai daganan suka wuce sama 4rooms ne asama ga masters bedroom nashi ga nata ga wasu dakuna biyu dayace anan su Amal zasu zauna daganan shida Aman suka wuce mosque dudda baya nuna mata komi but shigowanta gidan nan yakara tabbatar mata da Anty batanan duksai taji tadamu hankalinta yaki natsuwa sauka tayi itada Amali suka tafi kitchen kunga kitchen Ummi kawai tasaki baki suka kara fitowa waje wow gidan yahadu babban gaske yayi wani karamin kauye girma. Damuwa tama Hadiza yawa taki kwaso kayanta daga Abuja tasake dagewa da addu’a da sallan dare, tanason taje tasami Hajiya but batasan taya zata mata magana ba yau ne the second time datake kara nadaman rashin shirinta da kannen mijinta, ijiyan zuciya ta sauke ta dauki wayanta tareda dialing number Ya Aisha amman harya katse bata daga ba sauran biyu takira basu dagaba, saikuma kaman bazata iyaba taciro number Meena tai dialing shima harya katse bata dagaba kawai saitaji hawaye sun zubomata dasauri ta sharesu ta ijiye wayan ta buga tagumi tai shiruuuu tafara tunani zaka iya kai downgrading yan uwan mijinka kana ganinsu kaman bakomi ba sabida mijinki na sonka but the truth is kowa nada rananshi arayuwan nan always respect kowa ijiyan zuciya ta sauke kafin ahankali ta kwanta akasa kaman marainiya Mama tadade tsaye agaban dakin tasaga labule tana kallonta amman bata sani ba, tsakanin uwa da d’a sai Allah, Uwace aduniyan nan duk lalacewan danta tanason abinta haka, tafi kowa tausayin Hadiza da damuwa da damuwanta, shigowa dakin tayi ahankali ta zauna gece ta hakan yasa Hadiza ta dan dago kanta saikuma ta tashi zaune da wuri takalli Mama, hannu Mama takai takama kuncinta tace “Hadiza na kin ganki kuwa? Kaman bake ba kashe kanki zakiyi ne dukkin rame saikace wacce kanjamau ki kama kinyi duhu, baki iyacin abinci, menene Hadiza? Ki hakura da Nura mana tunda shi ya hakura dake? Allah zai baki wani mijin daya fi zama miki Alkhairi” dan lumshe idanu Hadiza tayi cikin sansanyan murya tace “Mamaa” saikuma kawai tafashe da kuka Mama tadade tana kallonta kafin kawai ta mike hijabin Hadizan ta dauka da car key dinta da aka kawo mata daga abujan dan dama a plazan shagonta tai parking motan tadauki wayanta duka tamika mata dasauri Hadiza dake kallon Mama tana kuka tace “Mama mezanyi dasu?” Ahankali Mama tace “tashi kije wajen Hajiya go and amend mistakes naki Hadiza” Shiru Hadiza tayi tana kallon Mama saikuma cikin wani kalan muryan ban tausayi tace “idan takoreni fa” ahankali Mama tace “tashi kije kozata koreki bakomi ta isa ne but ki sauke nauyin dakikejin nan azuciyanki and asked her for sincere forgiveness ba irin wanda kikayi a asibiti ba, kinji don’t be scared tashi kije Allah zai dauraki akanta zan miki addu’a” Hadiza kaman tayi mutuwan zaune saikuma ta tashi ta karbi Hijabin tasaka ta karbi wayanta tawuce tafita. Parking Hadiza tayi awajen gidan tadade zaune cikin mota sannan tabude kofa tafito jikinta duk yay sanyi kaman kankara dan batasan mezataje ta tarar ba tawuce tashiga gidan, matan datagani tsakar gida ta gaida tana tambayan ko Hajiya na nan aka cemata eh tawuce ciki sallama tayi agaban dakin daga ciki muryan wata mata ta amsa tace “shigo” ahankali Hadiza tacire takalmi tashiga ciki Hajiya tagani zaune kan kujera tareda wata mata wacce ita ta amsa sallaman tana nunama Hajiya wasu kaya da aka kawo ido cikin ido Hadiza tayi da Hajiya da sauri ta sauke kanta kasa matan tace “bismillah zoki zauna” wucewa Hadiza tayi tasami waje ta sauna akasa matan tace “bari naje Hajiya” Hajiya tace “to Salamatu ayi amfanida rabi kada ki manta” matan tace “to” tawuce tafita dakin yarage daga Hadiza sai Hajiya, ahankali Hadiza da kanta ke kasa tace “ina yini Hajiya” Kai tsaye Hajiya tace “lafiya lau Hadiza ya jikin naki? Naso zuwa dubaki amman kinsan kafan nawa maneji ne saisa, Allah yasa mai ceton ku ne sannu sannu”. 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣8️⃣ Why are you cheating on your husband?? “Sabida baya gamsar dani! Sabida yanada karamin gaba! Sabida he’s not romantic! Sabida baya bani kudi am suffering to feed our kids!”. Why are you cheating on your wife?? “Sabida tabude dayawa! Sabida bata iya kwanciya agado ba! Sabida she’s local batasan wassup ba! Sabida bata gayu! Sabida auren hadi ne! Sabida bata daukan bukatu na!!!” Kunsan this are the common reasons din da ma’aurata kebadawa na cheating??? Subscribe with 1k and read to learn chat me up now!! wa.me/+2347012181461 38 Dan kallonta Hajiya tayi ganin yanda kanta ke kasa yasa tace “tashi ki dauko ruwa da drink a fridge ki debo duk abinda kikeso a kitchen ni kadaine Meena batanan” girgizama Hajiya kai Hadiza tayi baki tabude zatai magana saita kasa Hajiya duk tana lurada ita amman tai shiru ta maida kanta kan tv, cikin wata kalan murya dake breaking Hadiza tace “Hajiya bansan ta ina zan faraba, yau kalamai sunyi karanci abakina dazan hada nabaki hakuri bisa kuskuren danamiki abaya” yadanyi shiru sabida muryanta was shaking sosai tace “Hajiya nasan nayi abubuwa da dama dasukasa kika tsaneni harda su Ya Aisha ma I called all of them dan nabasu hakuri harda Meena babu wanda yadauki wayana I understand no one wants me, Hajiya dan girman Allah dan darajan Allah Hajiya kiyakuri ki yafemin kuyafemin dukanku gabaki daya Haji…….” Sai kawai kuka ya kufcemata Hajiya tai shiru tazuba mata idanu dukta lalace kaman ba Hadiza ba, tabama Hajiya tausayi dan she’s a mother babu abinda kecin mutum kaman guilt din yama wasu laifi basu yafemai ba dan gyaran murya tayi anatse dan ba kwana kwana tace “stop crying Hadiza ya isa Allah ya yafemana Hadiza gabaki daya wlh har raina nayafe miki, su Aisha baki musu komi ba wayan nan, Nura ma inamai tabbatar miki shima ya yafemiki” Hajiya tadanyi shiru tana kallonta har ranta din tayafemata tace “amman Hadiza bazan miki karyaba banma d’ana sha’awan aurenki har abada!” Dasauri Hadiza yadago rinannyn idanunta tana kallon Hajiya data gyadamata kai tace “Mun yafe miki kuma bamu rikeki araiba, an riga an zama daya yanzu Hadiza kin haifamana yara so har lahira ana tare, amman dai babu zancen aure tsakaninki da d’ana yanda kikeson Aman da Amal yanda kikasan darajan su ki kasan zafin haihuwansu haka nasan na nawa dan, koda kin chanza hali Hadiza wasu tabon basa goguwa dan haka kitashi kije amman idan zancen yafiyane wlh tallahi mun yafemiki, yaranki kuma idan sukai Hutu zaa dinga kawo miki su idan kinason ki gansu call me ko wani cikinmu za’a kawo miki su” hade hannayenta Hadiza tayi dagudu zuciyanta har mata yakeyi kaman zai katse tazo gaban Hajiya tana kuka sosai tace “Hajiya ki rufamin asiri, Hajiya Nura kadai nakeso arayuwana dashi kadai zan iya zaman aure” Dasauri Hajiya tace “d’ana yahakura dake Hadiza, please mubar maganan nan tashi kitafi akwai mutane a tsakar gidan nan kar aji muryanshi a shigo adauka wani abune tashi kitafi” Hajiya tai maganan tana dafa kujera tana yunkurin tashi kama kafan Hajiya Hadiza tayi tace “Hajiya kiji tausayina ki kalleni amatsayin yarki” Dasauri Hajiya ta nuna Hadiza da hannu tace “kul! Karki sake ki kwatanta yarana dake sabida nabasu tarbiyan da sunsan banbancin matsayin namiji da mace! Kap yarana mata mazajensu ne jagororin su! Yarana bazasu taba yima mazajensu kazafi ba har abada wlh inaaaa! Basasu taba yima masajensu tabon dahar abada bazai bar sunan su ba! You have no idea kotun da shairin dakikama Nura yayi affecting nashi da business nashi kinsan investors nawa ya rasa? Sakenmini kafa!” Hajiya tamata tsawa dan batason tuna abubuwan da Nura yagayamata ya sameshi daya koma Abuja kwanakin baya, ahankali Hadiza tasaki kadan Hajiya idanunta sunyi jazur Hajiya tace “wallahi na yafe miki Hadiza kinji namiki rantsuwa hakama Nura ai ko darajan yaranki yakai mu yafemiki amman I will tell you this to your face dan bazan miki karyaba ko in yaudareki ko amafarki, ko amafarki Hadiza banama d’ana kwadayin ki kuma, sai anjima” Hajiya tawuce dakinta ahankali tareda maido kofa tarufe. Hadiza tai kuka tai kuka awajen na. Harta godema Allah takai almost 30min sannan ta tashi da kyar tawuce ta tafi bata damu da mutanen dake tsakar gidan ba haka tawuce, Hajiya tadade gaban dakin tanajin kukan Hadiza dake tabata kafin ahankali takoma bakin gado ta zauna tai shiru saida taji tafiyan Hadizan sannan tasauke ijiyan zuciya wayanta tadauka ahankali tai dialing number Nura. Ringing daya ya katse yakirata back ya gaidata cikin tattausan muryan irin conversation na d’a da mahaifiyarsa Hajiya tace “yanzu Hadiza tabar gidan nan” dan shiru Nura yayi baice komiba, ahankali Hajiya tace “tazo tabani hakuri kan komi dayafaru tama kira su Aisha wai tabasu hakuri amman duk basu dauka ba, Nura duk ta lalace” “umm” was the only thing daya fito daga bakin Nura dan shiru Hajiya tayi sai chan tace “Son I know nidakai we had this conversation before, nasan abubuwan da Hadiza tamaka hurt me deeply, and I support you dakace bazaka kara zaman aure da ita ba but I looked into her eyes today Nura I saw sincere nadama, wlh danasani ne cike tap a idanunta, koda naji haushi ina fushi da ita the decision is still yours Nura, kanason Hadiza ko baka sonta yanzu tell me the truth Nurudeen” dan shiru Nura yayi tareda lumshe idanunshi ya jinginar da kanshi jikin kujeran office din, kaman bazaiyi magana ba ahankali yace “I will always love Hadiza Hajiya, but har cikin raina nahakura da ita kaman yanda na fadamiki ranan, nabude new chapter in my life, na yafemata, I’ve moved on, bazan iya cigaba da zama da itaba anytime na kalleta I will remember itane the first person data taba zagina kala kala aduniya, the first matan data chakumeni, tamin kazafi tamin kotu, akwai somethings aduniya dahar kamutu kanaso but u will never get them sabida wasu dalilai I think Hadiza is just one, Hajiya inason Hadiza sabida bani nadaurama kaina son ba Allah ne shi kadai zai iya cire mini, but nahakura da ita har abada, please Hajiya kada ki karamin maganan ta” Ijiyan zuciya Hajiya tasauke tace “shikenan Nura, remember this kome kakeso I will always support you, all I want is inganka living peacefully and happily” anatse yace “Ummi is giving me that Hajiya, Ummi is the biggest gift in my life, yarinyar nan is just God sent, Hajiya she loves me unconditionally, duk abinda nakeso itama tanaso, she loves my children, zan biyamana aikin hajjin bana ma dukanmu mutafi harda ke Hajiya” murmushi tayi tace “Allah ya amsa, Allah yakaimu lokacin, Allah yabata yara itama” ahankali Nura yace “Ameen” cikeda so Hajiya tace “cigaba da aikin ka bari nadan kwanta” sallama sukayi daidai wayan Nuran na ringing yaga Baby dasauri ya dauka muryan Ummi yaji tana magana da kyar tana numfashi kaman wacce take kokawa tai numfashin da kyar tace “Da…….dyn Amal……” dip yaji shiru ga wayan na connecting dasauri ya mike yana “Baby, Ummi, Ummi” key mota kawai yadauka dasauri yashiga kiranta but ba’a dagawa 15mij yakaishi gidanshi yatafi side din Ummi aguje, yana bude kofa wani kamshin turaren wuta ya daki hancinshi, falon fess fess an gyara, sama yawuce yabude dakinta bata ciki shima agyare dakinshi yawuce kwance yaganta akan tile ga mop ga roban mop dudda ba ruwa akasa amman kaman zamiyewa tayi tafadi, tana nishi da kyar a sandare, dawani kalan gudu yayi wajen yadagota kadan kadan idanunta ke budewa arude yace “Ummi, what happen to you my baby?” Kallonshi takeyi but takasa magana sai hawaye dake bin gefen idanunta arude yashiga duddubata ganin kafafunta basa moving harta yatsunta ma, kawai ta sassandare kaman ice block yasa yaji gabanshi yadan fadi sai kawai yadauketa da sauri yakai mota yaja sai hospital aka shiga da ita ciki kusan 1hr yayi zaune Dr yafito suka wuce office nashi, Dr yabama Nura hannu yace “let’s start da good news your wife is 3month pregnant” dasauri Nura ya kalli Dr jikinshi har rawa rawa yake da mugun mugun mamaki yace “Dr wasa kakemin ne ko da gaske kake Ummi is pregnant”? Dr ya gyadamai kai yana murmushi hannu biyu Nura yadaura kan fuskanshi yace “Alhamdulillah, Alhamdulilah, Ya Allah thank you, Ya Allah nagode maka” he is seriously happy kaman zaiyi kuka, chan ya kalli Dr dake kallonshi yace “what’s the bad news Dr”? yayi maganan gabanshi na faduwa dum dum dum, ijiyan zuciya Dr yasauke yace “matarka is suffering from a very very rare disease, though bansan past medical history nata ba kota taba haihuwa” dasauri Nura yace “ta tabayi sort of sha she lost the baby at 6month hartai fama da yoyon fitsari” Dr yace “wow this information will go a long way it will help with investigation din dazamu mata” Dasauri Nura kirjinshi na dukan uku uku yace “to what’s wrong with my wife Dr? Lafiyanta kalau fa natafi office kaman faduwa tayi tana moping” ahankali Dr yace “I don’t think faduwa tayi datana moping, I mean she slipped and fall due to the watery ground I don’t think that’s the case here, your wife is suffering from HYPOKALEMIC PARALYSIS!” Wani kalan mikewa tsaye Nura yayi the only abinda ya gane a kalman is paralysis wato paralyze shiba science student bane amman kawai jikinshi saiyahau rawa kaman ba namiji ba da sauri Dr yatashi tareda kamashi yace “Alhaji Nura calm down is not abinda kake tunani zauna dan Allah calm down” idan kaga idanun Nura zaka tsorata yace “tell me Dr meya sami Ummi banni kawai ahakan am fine, tell me” yafadi maganan a hargitse, ahankali Dr yace “hypokalemic paralysis during pregnancy condition ne da bai cıka kama mata masu ciki ba, ba lallai nata yazama genetic ba sabida ciki yakawo mata halan, saimun gama investigation zamuyi ruling out” but amman condition din dake sanya numbness, weakness na muscles, nata akafane yanzu haka two legs dinta are paralyze which zamu fara treatment immediately once result are out, yawancin abinda ke jawowa mata masu ciki condition din nan is low pottasuim level, paralysis ba abu mai kyau bane gabaki dayanta wajen mai ciki, so just pray for her to get through this inba hakaba gabaki dayan 9month pregnancy dinnan a wheelchair zata yishi dan she will not be able to use her legs, sabida ko zatai amfani da kafan maybe tafara tafiya bazatasan lokacin da kawai kafafun zasuyi sanyi su daina aiki ba, hopefully bazaiyi spreading zuwa hannuwanta ba for now she can’t feel her legs, maybe kuma ciwon is related to abinda yasameta a first child nata so contact the hospital din dasukai managing nata lokacin su bamu medical history nata, it will help alot sabida musan menene complications datai having a first pregnancy dinta” baya Nura yayi dasauri Dr ya tareshi, ijiyan zuciya yasauke yashiga tattaba kujera kaman makaho yazauna akai da nata ya buga tagumi, ahankali yace “agida ta haihu, magungunan datasha ma alokacin na gida ne bana hospital ba, ba’a kaita hospital ba alokacin, Dr kall…….” Nura yayi shiru idanunshi sun cika da hawaye saikuma yakai duka hannayenshi biyu yakama hannun Dr yace “Dr you see that woman Ummi, my Ummi” yanuna kanshi yace “she’s all I got, she takes care of me, my mother, my kids my entire family, Ummi is just like my back born” yayi shiruuu saikuma yasaki hannun Dr yaki hannayenshi kan idanunshi yace “bantaba ganin a selfless human like Ummi ba, her heart is filled with love, peace and harmony, she loves kowa da zuciya daya, she don’t have a Mom nor Dad, itane first born, tanada 2 sisters, her grandmother look up to her, her sisters look up to her, my kids look up to her, my Mom and even me, ko sauro banso ya ciji Ummi sabida mutumce ita mai kashemana sauro idan yazo zai cijemu, how can I be here ina kallon Ummi tana paralyze eh Doctor”? Nura yayi maganan yana zaro handky da sauri daga aljihun shi, yakai kan idanunshi dasauri ya goge yace “Dr please help me, I don’t know do everything, idanma akwai hospital that are specialize in managing condition nata ko a outside Nigeria ne am willing to take her there I can’t stand watching Ummi na in pains, I can’t!” Nura yayi maganan gwanin ban tausayi. 💫 MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 3️⃣9️⃣ LABARIN FEMINIZM IS COMING TO AN END, CHAPTER2 IS AN ENTIRE DIFFERENT STORY ABOUT CHEATING🧡 KINDLY MAKE YOUR PAYMENT NA 1k and chat me up by clicking on this link; wa.me/+2347012181461 You can make payment 1k here 👇🏼 3107021073 Aisha Muhammad first bank KO 6353995766 M Shakur world Moniepoint Send evidence of payment I will add you to chapter 2 group. 39 Dafa kafadanshi Dr yayi yadan matse anatse yace “you have to be strong for her Nura, Ummi will be fine trust me, pray ciki yakawo mata ciwon idan shine tana haihuwa she will be fine just that dole ayi monitoring nata sosai da special kulawa, you can’t breakdown like this you have to be strong kanajina” Dr yadan jijiga kafadan Nura dake kallonshi kaman hoto, ahankali Dr yace “pull yourself together katashi muje” Nura yadade zaune awaje kafin yayi taking wani long breathe saikuma yahada hannayenshi yayi addu’a da kawai saiyaji yasami natsuwa wato Allah is just the best comforter, tashi yayi tsaye yakalli Dr yace “am ready” gyadamai kai Dr yayi yace “let’s go” wucewa sukayi suka fice tare zuwa private room da akai admiting Ummi tana kwance an mata fixing drip tana bacci, sosai Nura ke kallon fuskanta gaban gadon Dr yaje inda kafafun Ummi suke yasa hannunshi gaban riganshi ya cire pen dinshi yakai tafin kafan Ummi ya sosa but batai motsi ba tattaba kafafun yayi duk Nura na kallo batai motsi ba sannan yazo inda Nura yake yana kallonshi kaman gunki murya chan kasa yace “I assure you everything is gonna be fine okay, bari naje naji how far da lab investigation danace ayi” gyadamai kai Nura yayi yawuce yafita daga dakin ahankali Nura yaja kujeran gaban gadon ya zauna tareda kai hannunshi yakama hannun Ummi ahankali yadaga yana kallon fuskanta yakai kan bakinshi ya manna ma kiss saikuma ya kwantar da fuskanshi kan hannun nata yana kallonta ahankali yace “you are not alone Ummi, we will get through this together, you have to fight for me, for our baby” yakai dayan hannunshi yadaura kan cikinta yace “for our baby” yadan lumshe idanu yace “for Aman and Amali, for Gwaggo and su Shatu, for Hajiya and all my family Ummi, you are a strong girl fight kinji” yay maganan yana mammanna ma hannunta kiss kaman zai hadiye, ahankali Ummi ke bude idanunta kanta yamata nauyi tana kokarin tuna abinda yasameta tasan tagama gyaran falo tazo sama ta gyagyara tana dakin Baban Amali shima ta gyara tana cikin moping taji kafafunta sun rike sai chan sukai sanyi kaman kankara kawai taji tazube dudda tai kokarin tafadi kan hadi but takasa motsi da kafafun at all tadau waya daganan batasan meya faruba tasss tabude idanunta takalli saman dakin, dumi dataji da lema lema a hannunta yasa tadan juyoda kanta gefe Nura tagani zaune yakama hannunta ya rungume gamgam a fuskanshi ya lumshe idanunshi hawaye suna gangarowa ahankali suna zuba saman hannunta faduwa gabanta yayi dasauri tabude bakinta gabaki daya batada karfi takeji kaman an kashe mata jiki tace “Baban Amali” dasauri Nura yabude idanunshi yakai hannunshi dasauri yana share fuskanshi yakalleta tareda mikewa yana shafa mata fuska cikeda so yace “Baby na kin farka” gabanta na faduwa sosai ita bawai ciwon ko asibitin dataganta viki ke damunta ba no kukan dataga yanayi cikin saryin murya tace “meya sameka kake kuka”? Dan zaro idanu yayi ganin yanda take kallonshi hankalinta tashe kuma yasan dan raga hawaye a idanunshi ne yasa yadanja hancinta yace “common da girmana zanyi kuka saikace ke, I think idanuna ke ciwo nagama da nan zanje office na likitan idanu yadubani” bata taba karyata shi ba so she believe cikeda so tace “sannu muga idanun wani abu ya shiga cikine” tai maganan tana daura hannayenta and kan fuskanshi zata budemai idanu dasauri yakama hannayen yace “I am fine, meya sameki ya akayi kika fadi?” Dan kallonshi tayi ahankali tace “ina moping daki shine kawai naji kafafuna sun daina aiki sun dawo kaman kankara daya daskare gabaki daya ina kokarin najasu naje kan gadoma nakasa shine na zube, kaman nakiraka ko?” Gyadamata kai yayi ya manna mata kiss a goshi yace “don’t worry kafanshi will be fine okay” gyadamai kai tayi takalli kafan sannan takalleshi tace “har yanzu kaman daskararren kankara sukemin” tashi yayi saiyazo wajen kafan ya nunasu da yatsa yana daure fuska yace “ku kafafun Ummi me kuka damun mini mata”? Wani kalan murmushi Ummi tayi tana kallonshi, ganin tai murmushi yace “idan baku barta ba zaku gamu da fushin Noor din Ummi tom” for the first time ta kyalkyace da dariya tace “kafafu kuce munji Dadyn Amali” Dan dariya shima Nura yayi yadawo gadon yazo gefenta ya zauna yana kallon fuskanta yace “nabaki good news”? Dasauri ta gyadamai kai tace “eh” murmushi yamata hannunshi ahankali yakai yadaga riganta sama yakalli flat tummy dinta ahankali yasa hannunshi yakamo nata yadaura akan cikin kafin yasa nashi akai yakalli fuskanta yanda take zaro idanu tana kallonshi takosa yafadi abinda zai fadi ahankali yace “nan da wata shidda Babyn mu zaizo duniya” dasauri Ummi takara zaro idanu tana kallonshi bakinta na rawa sosai, tanason tai magana ma takasa Nura yace “kina dauke da cikin 3months Ummi, my baby na cikin cikinki” fashewa Ummi tayi da kuka tana dariya arayuwan ta tana son yara kodan babynta na farko yakutu ne oho but tanason yara cikin yakara kankamewa da hannun Nura tace “babyn ka, Babyna, babyn mu?” Gyadamata kai yayi yace “yes Ummi” dariya tafashe da shi sosai hawaye na fitowa daga idanunta suna ahaka akai knocking dakin hakan yasa yazare hannunshi tareda rufe mata cikin daidai Dr na bude kofa yakalli Nura yace “come with me Nura” ganin Ummi ta farka yasa yashigo yace “Madam kin tashi ya jikin?” Ummi na murmushi sosai tace “lpy lau” Nura Dr yakala alamun yabiyoshi Nura yakalleta yace “bari naje nazo” gyadamai kai tayi kaman yar baby, Office suka shiga Dr yace “some of her lab results are out” dan faduwa gaban Nura yayi yakalli Dr dake dube dube, sai chan yayi shiru tareda ijiye file din yashiga typing a computer shi yayi printing wani paper yadauka tareda bawa Nura dake kallonshi yace “Nura we have to start treatment na matan ka immediately, zamu riketa a hospital for as long as needed ni karan kaina bazan iya gayamaka ga randa zamu sallameta ba, paralysis nata is spreading yanzu yakai cinyanta, before dakika shigo it was below knees nata, kaje pharmacy get all this including pampers na manya” dasauri Nura yakalli Dr, ahankali Dr yace “yes, we will not risk tana tashi for anything ba, Nura anything dazaisa Ummi tafadi can kill Babyn datake dauke dashi so she needs good management, the good news is I don’t think is genetic though munakan bincike har yanzu but ciki ne yasamata abin zai iya tafiya any moment idan kuma bai bartaba dazaran ta haihu zai saketa” Dr yadan sauke ijiyan zuciya ahankali yace “do you want me to tell her abinda ke damunta ko na barka kayi?” Kasa magana Nura yayi Dr yace “bamason anything dazaisa BP ta yayi raising dazaran hakan yafaru zai bata mana komi it will worsen this paralysis wlh, she needs kwanciyan hankali, zaka iya ka sanar da ita batare daka dagamata hankali ba ko ni namaka?” Ijiyan zuciya Nura yasauke kafin ahankali yace “zan sanar da ita” gyadamai kai Dr yayi yace “get everything ka sanar da ita nabaka 1hr, calm her down everything zamuzo mufara treatment” gyadamai kai Nura yayi yatashi yaje pharmacy yasayo komi kasa karban kayan yayi yace “su rikemai yana zuwa yawuce motanshi ya şairi ya shiga ya zauna tareda kunna motan ya kunna ma kanshi AC” wayanshi yaciro dasauri yaciro number Hajiya he just needs energy shima ringing daya Hajiya tadaga tace “Nura” cikin wani kalan weak voice yace “Hajiya” muryanshi kadai taji tasan ba lafiya ahankali tace “menene Nura why do you sound down” Dan lumshe idanu yayi ahankali yace “Ummi” faduwa gaban Hajiya yayi dasauri tace “what happen to Ummi”? Da kyar Nura ya iya ya gayama Hajiya komi, cikeda hikima irin na manya Hajiya tace “it’s okay Nura calm down ciki babu kalan abinda baya sanya ma mace, you have to be strong for her kaji, kaje ka sanar da ita kadena bata lokaci anjima zamuyi magana da kyau, tashi kaje yarona Allah maka Albarak, Allah bama Ummi lpy” katse wayan yayi yawuce ciki komi yawuce dakin dashi nesa da Ummi ya ijiye kayan daketa kallonshi kawai jitayi gabanta na faduwa dudda he’s smiling but body language nashi na gayamata wani abu, tanada this connection da Nura whenever he’s happy she senses it hakama whenever he’s sad, dawowa yayi bakin gadon ya zauna yace “yammata na” murmushi tamai takama hannunshi tarike anatse tace “meke damuna?” Kaman daga sama yaji tambayan sai kawai yaksa magana kaman an rikemai baki, Ummi na kallon kwayan idanunshi tace “banda Babyn mu inada wata cuta ajiki ko?” Kasa magana still Nura yayi, hawaye ne masu dumi suka sauko daga idanunta ganin yaki magana, dan lumshe idanunta tayi sannan tabudesu tareda sauke ijiyan zuciya takai hannunta ta share fuskanta tass sannan tai murmushi takai hannyenshi data rike tadaura kan kumatunta taji wani sanyi har ranta takalli fuskanshi ahankali tace “mutuwa zanyi ko Baban Amali!” Dawani kalan sauri Nura ya fizge hannunshi daga kan fuskanta yasauka daga gado yamike tsaye yace “noooo!” Fashewa da kuka Ummi tayi mai tsuma zuciya tace “ni naji ajikina mutuwa zanyi, alamomin zare rai daga jikin dan adam shine akashe wanan gaban akashe wancen gaban har a idasa zare ran, dafarko ai kafafuna ne sukai sanyi yanzu har cinyana bana jinsu kwata kwata kaman ba’a hallici wajen ba ajikina haka nikeji, mutuwa zanyi wal……..” dasauri Nura yasa hannayenshi biyu yadaura abakinta yamata wani kalan tsawa. “Shut up!” Ranshi abace yace “kimin shiru kika kara wani magana adakin nan saina sabamiki kinajina” yayi maganan hawaye suke cika a idanunshi sosai yana kallonta, fashewa Ummi tayi da kuka sosai dake gangarawa ta gefen idanunta ahankali tasanya hannunta ta cire hannayenshi dagakan bakinta ta mannasu a kumatunta duka biyun tana wani kalan kuka harda shesheka tana kallon idanunshi kaman yanda yake kallonta yakasa magana, cikin kuka tace “Baban Amali ina sonka sosai” tana wani irin kuka tace “inason inga Gwaggona da su Shatu, ka kiramin su banson nabar duniya bangansu ba su kadaine yan uwana, Baban Amali inason inga Gwaggona ka kawomin Gwaggona da kannina kaji” Nura shida akace he should be strong saiyaji baimasan menene strong ba, cikin kuka tace “nadade inason namaka wata magana but nakasa kona fara baka bani hurumin yinta Baban Amali kana sona”? Gyadamata kai yayi yama kasa magana cikin wani kalan kuka ta rirrikemai hannuwa gam a kuncinta tace “indai kana sona to kadawo da Anty! Kadawo ma dasu Aman Maman su, nasan baka tareda ita, Baban Amali nasan menene girma ba mahaifiya dudda ina tareda Gwaggo dake sonmu but kullum muna cikin kewan maman mu, duk yanda nakai ga son su da yanda su Hajiya suke sonsu bazamu taba iya maye gurbin mahaifiyansu ba, rayuwa daka gani kowa da kaddaransa abinda Allah ya rubuta saiya faru, Nura wani zubin munayin abu koda zuciya mu bataso dan ta farantama wayanda muke tareda su, Anty nada fushi but Anty Mutum ce! Anty nada fada but Anty nada kirki! Bata taba samin ido ba, ta yarda dani, ta sakan mini yaranta batare datamin shamaki dasu ba, bata tabajin haushin yanda suke sona ba, Baban Amali inhar kanasona da gaske inhar inada kima da daraji awajenka daidai da kwayar zarra, inhar ka yarda da son danake maka da wanda nake masu Hajjya dasu Aman kadawo da Maman su inaso koda zan mutu nasan nama yaran danake bala’in so aduniya abinda yakamata, Baban Amali dan girman Allah kadawo da Anty……..” hannunshi yadaura abakinta hawaye nafita daga idanunshi dasauri tacire tarike hannun, tace “kanason Anty har gobe har jibi, wazai kula dasu Aman yanzu? Wazai bama yarana yarana abinci? Wazai musu oyoyo daga kofa idan school bus yadawo dasu, Nura kalleni” Ummi tai maganan tana kallonshi ganin ya runtse idanunshi, cikin wani kalan murya tace “kome zakayi arayuwan nan kadinga tuna Aman da Amali, rayuwanka belongs to them, suna bukatanka da mahaifiyar su at this stage dasuke, kaga babynan” tanuna cikinta sannan tadanyi murmushi majina na gangarowa daga hancinta tace “banjin zan haifeshi bama Baban Amal kaman dashi zan mutu yana jikina” wani kalan iska Nura yahuro daga bakinshi irin iskan nan nakanaso kahana kanka kuka yakasa magana, cikin harshen turenci danta soma picking some words due to school dasukai itada Meena akano tace “I’m dying Nura! Ummi is dying Baban Amali!” Wani kalan zubewa knees din Nura sukai akasa yayi kneeling yana kuka hannuwanshi har lokacin Ummi tarike gam akan fuskanta tace “abu biyu zuwa uku nakeso kamini nafarko Gwaggona da kannina ka kawomin su nagana dasu muyi bankwana! Nabiyu kadawo da Maman su Amali dan Allah itama inaso nai bankwana da ita, na uku inaso kadena kukan nan kaji Mijina” . Ummi crush every single emotion na zuciyanshi he’s shaking and crying shi kadai yasan yanda every single word nata ke piercing zuciyanshi, Banda mahaifinshi daya rasu baitaba loosing wani close one ba, yau this whole scene reminds him of ranan da baban shi yarasu shima fa lafiyanshi kalau har yaje school yana dalibai lectures yadawo sai ciwo na less than 1hour sai rasuwa she’s just reminding him of everything sakin hannunshi tayi ahankali tana kuka ahankali yajaye hannunshi shima dake rawa yasa a aljihu yaciro wayanshi yafito da number father Inlaw ringing biyu zuwa uku Baba yadaga kai tsaye Nura yace “Baba inaso ka daura min aure da Hadiza zan turo wani ya wakilceni idan aka daura inaso ta taho Abuja yanzun nan Baba, zan kirata yanzu naji nawa takeso sadaki saina turo” Baima jira amsan Baba ba yashiga danna numbers din Hadiza dake kanshi yamike da kyar tareda manna ma Ummi kiss a goshi yace “ina zuwa” gyadamata kai yayi haryakai kofa tace “thank you Baban Amali” kasa kallonta yayi yawuce yafita yayi dialing Hadiza na kwance lamo kan gado a dakinta Anty Jams na gefenta dake famada ita taci abinci taki wayanta ya shiga ringing ko kallon wayan bataiba harya katse jin ana sake kira yasa Anty Jams tadau wayan tace “wai bazaki daga wayanki b…..” kasa karasa maganan tayi ganin Nuri ke kira dasauri tace “ke Nura ke kiranki” awani kalan daburce Hadiza ta tashi ta fizge wayan jikinta da hannunta har rawa suke ganin Nuri ke kiranta daukan wayan tayi yana gab da katsewa taki wayan kunnenta tace “Hel…..Assalamu Alaykum” cikin sassanyan murya taji maganan Nura yace “Hadiza zaki aureni”? Hadiza jitayi numfashinta zai tsaya, sai bakinta yashiga rawa tama kasa magana tsabagen shock, ahankali Nura yace “I want to marry you idan you want to come back to me, inaso kidawo Abuja yau, I need you Hadiza!” Nura yayi maganan asanyaye kaman baitaba fada da ita ba, cikeda shaukin so Hadiza tace “yes Nura zan aureka” ahankali yace “nawa kikeso sadaki” ahankali itama tace “200k nakeso sadaki” ahankali yace “are you ready to be my wife this time around?” Ahankali Hadiza tace “I am ready to be your wife and serve you Nura till eternity” lumshe idanu yayi ahankali yace “Ummi is sick Didi” faduwa gaban Hadiza yayi dagajin yanda yayi maganan tasan ba lafiya, cikeda son mijinta tace “subhnallahi meya sameta Nura”? Cikin tattaushiyan murya yace “idan kika iso zan gayamiki, Hadiza I want you to be the wife that I’ve always dreamt of, I want you to support me, and to accept me kaman yanda I will always do all of that for you” cikin tsantsan so da kauna tace “Nuri this time auren bautan Allah zanyi adakin mijina not awani, I will be the best wife for you, you will be the husband and lead me, zamu kula da Ummi tare I promise you” in a very sweet voice yace “thank you My Didi, zan tura miki sadakin ki and your ticket okay, I’m sorry bazan sami daman zuwa ba ina asibiti” cikeda so tace “I understand Nuri na! I love you regardless, just take care of Ummi saina shigo” ya katse, wayan Anty Jams da mamaki ya kasheta ganin matured Hadiza for the first time in decades tace “ahh kinyi hankali kene zaki kula da Ummi”? Anty Jams ta kalla tace “I’m ready to do everything for Nura Anty Jams nida feminizm har abada I will serve my husband like never before I will be his strength koma menene damuwan, ina kishin Ummi har gobe har jibi, but mijina ya zabeta bazan tsaneshi because of that ba, and koma menene ke damunta i sincerely wish her quick recovery, i am a new Hadiza, and I will make my husband yasoni sama da baya” daidai Baba na kwala mata kira wani wani murmushi daidai lokacin alert na 200k na shigowa wayanta tace “the moment is here Alhamdulillah! Ya Allah na gode maka da second chance din nan daka bani, bazan kara kaurace maka ba, ya Allah kabani juriya da hakuri da kwazo da zama da Mijina da kishiyata ya Allah ka zaunar damu lapiya, kabawa Ummi lpy, Karagemin kishi, ka sakamin abinda Zeenah tamin, bye bye zawarci”. Anty Jams ta kyalkyace da dariya ganin how happy she’s. Nura loves Ummi❤️ Nura loves Hadiza❤️ Nura loves matayenshi❤️❤️ IS UMMI DYING?💔💔💔 💫 MATAN?? Ko MAZAN?? 💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 4️⃣0️⃣ Kina neman class na matan aure da akeyi da turenci??? To look no more ga MAJAL WELLNESS nakawo muku💃 Indai class ne da ake tafarfasa karatu kan harkan abenga da turenci trust me bazaki taba samin a class better than SAMOHHACK by Majal ba so hurry and join her waitlist group ko kiyi chatting nata up now now now!!! wa.me/+2349043619538 Check out her IG page @majalwellness💃 You will come thank me later oo💃 https://chat.whatsapp.com/H50w7C7Lrbv8ZiPKzKxm5l Ijiyan zuciya yasauke bayan yagama magana da Hadiza kafin ahankali yayi dialing number Hajiya ringing daya ta dauka kaman daman wayan na hannunta tana jiran kiranshi ne tana dauka tace “Nura ya jikin ka sanar da ita yakukayi?” Dan shiru Nura yayi kafin ahankali yace “Hajiya Ummi Ummi……” saikuma yayi shiru, ahankali Hajiya tace “talk to me Nura, meya sami Ummi? Metace”? Cikin very breaking voice yace “she begged me to do 2 things for her wai tanaji ajikinta mut……” “ba abinda zai sameta!” Hajiya tafadi cikeda damuwa, Nura yace “tace nadawo da Maman su Aman, sanan nakira mata Gwaggon ta da kanninta” dan shiru Hajiya tayi sai chan tace “Nura Allah kyautan Ummi kawai yadauka yabaka, nadade banga mace irin ta ba! Zuciyarta Alkhairi ne cike acikinta kuma da izinin Allah bazata mutu ba, Nura idan namiji yaşamı mata tagari sai ya kasance miji nagari agareta ance kyawun tukuici godiya hope ka kira Mahaifin Hadiza ka sanarda shi” gyadama Hajiya kai yayi kaman tana gabanshi yace “nakira amman banda wanda zai wakilceni Hajiya” Dasauri Hajiya tace “zan tura Murtala da Shamsu” ahankali yace “thank you Hajiya” ahankali Hajiya tace “thank you for honoring maganan Ummi, I feel very proud of you ina matukar alfahari dakai Nura, Ummi zata samu lpy kuma dukanku zakuyi zaman lafiya kaji, gobe muma ina ganin zamu shigo, yanzu wazaka tura yaje yadauko maka su Gwaggo a kauye” ahankali yace “yanzu zan kira Alhaji Musa” Hajiya tace “to shikenan” sukai sallama yashiga kiran Alhaji Musa cikin 30min aka daura auren HADIZA da NURA akan Sadaki 200k bata dauko komi ba banda handbag dinta wani lafiyayyen ubansun abaya tasaka su Baba suka mata fada da wa’azi Baba yakaita airport tahau jirgi sai Abuja tana kaina taga manager Nura yazo daukanta sai murmushi take school na yaran tawuce tadaukosu suka wuce sabon gida dan nan Nura yace tazo gateman yabude mata side nata tashiga ga set na akwati sababbi guda 6 afalo aksatın dayay order since bayan auren Ummi ne dan baisamu yamusu akwati ba, yaran tagama attending to them ta shiga kitchen da kanta dan musu girki da wanda zatakai asibiti. Dakin Nura yakoma bayan yayi sallan azahar a mosque samin Ummi yayi tana bacci, yana zuwa yakama hannunta dasauri tabude idanunta takalleshi murmushi yamata yace “natasheki?” Girgizamai kai tayi daidai wata Nurse tashigo tawuce wajen ledodin asibitin da Nura yakawo tana ciro ledan pampers tace “Yallabai can u excuse us zan shiryata ne?” Kallon Pampers din da rigan asibitin Nura yayi ahankali yatashi tareda mika mata hannu yace “bani zan shiryata dakaina” kallon Nura nurse din tayi saikuma tabashi ahankali tace “bari nabaku wuri” wucewa tayi tafice yaje wajen kofan yarufe tareda murza key yadawo gaban gadon ya kalli Ummi daketa binshi da idanu yace “na shirya ki?” Gyadamai kai tayi ahankali tana kallonshi tsayawa yayi shiru yana. Kallon fuskanta kaman yanda take kallonshi kafin ahankali yace “I love you Zainab” sake lumshemai idanu tayi tabudesu ahankali wani boturi ya danna agadon, gadon yataso kaman kujera hannunta yakama yasa tabayanshi ya kwantar da kirjinta ahankali nashi yasa zip gently yabude rigan hannunshi yakai yayi unhooking brlack bra dake bayanta ya maidata jikin gadon tareda zame rigan daga hannunta ahankali ya zame bra dinma ijiyan zuciya yasauke yasake danna botur din ya kwantar da gadon kafin gently with so much care kaman zai daga kwai yakama jikinta ya juyarda ita side, Ummi jitayi hawaye yazo mata ganin yanda ake mata komi kaman gawa, zip din skirt dinta yaja kasa sannan yazo takama yazame skirt din yana kallon black pant din dake jikinta dan ijiyan zuciya yasauke ahankali ya kwabe mata, sannan yadauki pampers din yakalla kafin ya kalleta hawaye yaga sun zubo daga idanunta dasauri ya daure shi asanyaye ya sakamata yadauki gown din yasamata shima yana kallon yanda hawaye ke fita daga idanunta sanan ahankali yazo kusada ita kawai ya rungumeta kaman jira take fashewa tayi da kuka sosai a kirjinshi yanajin yanda hawayenta ke jikamai gaban riga murya chan kasa yace “it’s okay, ya isa am here for you kinji, babu abinda zai sameki is okay” bayanta ya bubbuga yana shafawa ahaka akı knocking dakin maidata yayi ya kwantar ya kwashe kayanta ya linke tsaf yasa a wardrobe na dakin sannan yawuce kofan yabude Doctors guda uku ne da nurses hudu suka shigo akasa Nura yafita. Yana zaune awajen wayanshi yahau ringing number Hadiza ne hakan yasa yadauki wayan cikeda so tace “gani a asibitin Nura nakawo muku abinci kana ta ina” ahankali ya mike daga inda yake zaune yace “ina zuwa” katse wayan yayi yana tafiya ahankaali yafito daga ta wajajen parking space ya hango Hadiza tayi parking wani motarshi datazo dashi tafito rikeda basket a hannunta tana waige waige yadade yana kallonta kafin yakarasa saida yakawo ta wajajen taganshi hada idanu sukayi for the first time in her life saitaji tana wani jin kunyanshi da nauyinshi tuna abubuwan datamai hakan yasa takasa motsi sai kallonshi datake wani kalan wutan sonshi na tashi azuciyanta, anatse Nura yakarasa gabanta ya tsaya chak yana kallonta kasa daurewa kallon tayi da sauri tasauke kanta kasa ahankali tace “ina yini Nuri, yamai jiki?” Kara one step Nura yayi kafin ahankali yawani kalan bata warm hug Hadiza jitayi jikinta yasaki gabaki daya she missed her Man, she missed his body this thight hug just gave her the comfort data dade bataji kalanshi ba almost 30secs yayi ahaka da ita kafin cikin wani cool calm voice yace “welcome Didi, how was your flight”? Ahankali tace “smooth ya jikin Ummi?” Gyadamata kanshi yayi tareda dauke ijiyan zuciya ahankali yace “Alhamdulillah, let’s go” yasaketa tareda sa hannunshi daya ya karbi basket din dake hannunta yasa dayan hannunshi yakama hannunta suka wuce ciki ahaka bini bini take kallonshi yanzu take kara ganin abinda tayi loosing Nura is a man dazai kula da matarshi ba ruwanshi look at yanda ya karbi basket din daga hannunta to da dataketa kukan feminism mema exactly take nema dan Nura always treat her like a queen, gaban dakin sukaje daidai zai bude kofan ta karbe hannunta daya rike dasauri dan yanzu she’s a change person tasan Nura nasonta no need to show Ummi ko the world yana sonta banda hai bazataso ta sama mara lafiya bakin ciki ba koyaya badadi kaga mijinka na lovi dovi da kishiyahka tasan zafin hakan sama da kowa dan juyowa yayi ya kalleta him ta karbe hannunta kafin ahankali yabude kofan dakin ya shiga ciki Ummi ce kadai adakin su Dr basu dade da fita ba an samata drip guda biyu a manna mata wasu abubuwa haka akafan da massage sukeyi tsotse hakan sukayi oho bata saniba dan batajin komi ganin Hadiza yasa tasauke ijiyan zuciya ahankali Nura yazo gadon da sauri yaduko da kanshi saitin nata kaman zai hadiyeta yace “ya jikin wani abu namiki ciwo?” Girgizamai kai tayi alamun a’a, ahankali yace “Dr yamiki allura”? Sake girgizamai kai tayi yace “ga abinci Hadiza ta dafa miki zakici” gyadamai kai tayi ahankali takalli Hadiza data tsayavtana kallonsu ahankali Ummi tace “An……ty” matsawa Nura yayi hakan yasa Hadiza ta tako tazo gaban gadon taja kujera tazauna tana kallonta cikeda kulawa dakuma mutuntawa tace “yajiki Ummi sannu Allah baki lpy Allah kara sauki”. Ahankali Ummi tace “Anty har yanzu kina fushi dani?” Dasauri Hadiza ta girgiza mata kai tace “no banayi Ummi” har ranta kuma batayin dan Ummin tabata tausayi hannunta Ummi takama tarike tace “kiyafemin idan nataba batamiki rai please” dasauri Hadiza tace “nayafe miki nima kiyafemin all abubuwan dana miki Ummi kinji” gyadamata kai Ummi tayi tace “Nayafe daidai lokacin Nura yakawo plate na rice din da stew daga gadon yayi kaman dazu yazauna akatifa gefen Ummi yace “bude baki kici haaaaaam” ahankali Ummi tabude baki yasa mata tadanci like 4spoons tace ya isheta juice din tasha sosai ahaka azaunen Nura na gefenta rikeda plate wayanshi yahau ringin yadauka ganin Alhaji Musa ne that means yasauka a Adamawa jin saukan kan Ummi a shoulder shi yasa yakalleta ganin tayi bacci yasa yamikama Hadiza plate din yasauka yana magana da Alhaji Musa ya kwantar da gadon yarufa mata bargo da kyau yagama wayan abakin gadon yazauna yakalli Hadiza sai kawai yaja mata hancı dan murmushi tayi tace “bari nakoma gida yaran nan su kadai nabari” Gyadamata Kai yayi yace “muje narakaki” har mota yarakata takoma gida, babu wani available flight daga yola to Abuja dole sai gobe zasu zo. Shiya kwana da Ummi shiya sake chanza mata pampers bayan ya tsaftace mata jiki yamata alwala tayi salla anan kwance agadon suka kwana tana jikinshi. Cikin dare firgitan dayaji tayi ya farkan dashi bude idanunshi yayi yakalleta idanunta a lumshe but jikinta yayi zafi kaman wuta lips dinta sun bushe kaman basu taba ganin ruwa ba daidai lokacin Nurses sukazo dubata arude Nura yace “kudubata pls” tamper türe ta kadai suka duba akace akira Dr, Dr nazuwa sai akahau cema Nura yafita daga dakin arude Nura yace “what happen” fitar dashi Dr yayi yace “I will explain anjima” yakoma dakin da sauri Nura rasa inda zai sa kanshi yayi chan saiga Dr yafito Nura yabi shi dagudu zuwa office dinshi Dr yace “Nura condition din wife naka yakai hannayenta” baya Nura yayi zai fadi yadafa banyo da sauri yana nishi da karfe yana addu’a Dr yace “but we are trying our best Kari damu, jeka ganta” da kyar Nura ya iya daga kafanshi yafice daga office din yatafi dakin yana kallon Ummi idanunta a lumshe ga hannayen kaman sanda ajiye gefenta juyawa yayi dasauri ya kalli kofa yadaura hannunshi kan bakinshi saikuma yajuyo yazo gaban gadon tazuba tagumi yana kallonta kaman ciwon yadawo jikinshi yakeji, kaman ba Ummi daya tafi office ya barta lafiya agidaba kaman tai ciwon shekara wannan wani irin paralyze ne Innalillahi har gari yawaye baccin dabaiyi ba kenan yatafi mosque bayan yakira Hajiya itama tace “gatanan zuwa garin”. Wuraren 6:30 yadawo dakin idanunta biyu amman sun kankance looking so weak Allah kadai yasan meke mata ciwo, yunkurin amai takeyi anan kwance da güdü yayi gaban gadon dan bata iya daga hannu ko kafa kaman jaririya dagota yayi yadauki Rohan amai na hospital yatara tadingayi anan she’s so weak kaman paper yadanna bell nurses sukazo suka tayashi tai aman tagama aka bata ruwa da kyar ta iya bude bakinta tace “Gwag…….g……” hannunta Nura yakama gam yace “tana hanya kinji” lumshe idanu tayi ta bude alamun to. Wuraren 8 Hadiza tashigo hospital din takawo musu abinci takwoma Nura another set na cloth itama yanda taga Ummi saida taji kuka yazomata Nura yahanata yi karşı tada mata da hankali around 10 na safe Alhaji Musa yashigo asibitin dasu Gwaggo dasauri Nura yabar Hadiza da ita dan zuwa shigowa dasu. Gwaggo na sanye da atampa mai kyau an mata dinki Bubu da Zani dawani dan Madinan silipas akafanta ta yafa farın lullubi aka, same with su Shatu suma irin atampan Gwaggo ne ajikinsu sai lalle lalle suke a tsakar hospital din Gwaggo na hango Nura kafinma yakaraso ita tafara tafita dasauri gabaki daya hankali ta tashe tana kaiwa dan dashi tace “ina jikana?” Ajiyan zuciya Nura yasauke yace “tana ciki Gwaggo sannu da zuwa” gyadamai kai Gwaggo tayi ta wuce Nuran tayi inda taga yafito kaman tasan dakin bata damu da yanda ake kallonsu ba dasauri Nura yabiyo bayanta shikuma Alhaji Musa yakalli Shatu da Zakiyya yace “ku muje masu kuka a jirgi” binshi sukayi, suna zuwa ciki Nura yabude kofan dakin Gwaggo tafada ciki kaman an jefata tashi Hadiza tayi daga kan kujera tana kallon tsohuwan tace “sannu da zuwa Gwaggo” jin an ambaci yasa Ummi tabude idanunta kadan tajuyo Gwaggonta tagani tsaye gaban kofa ta dafa bango tana kallonta ga Nura a gefenta gasu Shatu abayanta, kokarin daga hannayenta take tamikama Gwaggo takasa gwanin ban tausayi hakan yasa Gwaggo ta daga kafa tafara tafiya ahankali har zuwa gaban gadon sai kawai ta tallbo fuskan Ummi cikeda so ta goge mata fuskanta tasss tace “dena kuka Gwaggon ki tazo ko yanzu” ta dago kanta takalli Nura da Alhaji Musa tace “kuzo ku dauketa ku kaimin ita mota mukoma kauye na nema mata magani” dasauri Nura yataho wajen hakama Alhaji Musa anatse Nura yace “Gwaggo nan asibiti ne bakigama Karin ruwa ake mata ba ki barta anan Gwaggo” cikeda masifa tace “kai kaga jikin jikana ne, yooo asibiti da alluran nan nasu kara mata karfin ciwo zasuji, dauji ne ciwon nan muna zuwa kauye dakaina zan shiga daji na samo mata sassake assake na magungunan na jika dana sha dana shafawa kafin kace mene zata warke” cikeda lallabawa Alhaji Musa yace “Gwaggo to shikenan ki bari agama na nan saiki tafi da ita kauyen” fashewa da kuka Gwaggo tayi Tana nuna Ummi dake kallonta da kyar tace “yarinyar nan haka ciki ke wahalar da ita, kubani ita natafi da ita kauye nasama mata magana iyye, Shatu keda Zakkiya kuzo ku cicciba mini ita abaya na goyata mutafi tasha ai Alhamdulillah nayo guzurin kudina, kuzo ku cicciba mini ita abaya” zasu fara tahowa da sauri Hadiza tasa baki hannun Gwaggo takama cikeda lallashi tana magana ahankali kaman mai whispering but zaka iyaji tace “Gwaggo kiyakuri kinga kukanki zai kara tadama Ummi hankali hakan baida kyau agareta, yanzu kiyakuri tadanji sauki koda kadan ne saiki tafi da ita, yanzu kinga ayanda take zaman mota kona jirgi zai mata wuya ko Nuri” dasauri Nura shima cikeda lallashi yace “eh Gwaggo kiyakuri kinji, yanzu kiyi magana da ita tun jiya ketaketa nema” juyawa Gwaggo tayi takalli Ummi tana kuka sosai Hadiza tasaki hannunta, bayan riganta tasa ta share idanunta tass sannan tazo gaban gadon ta duka ta shafa fuskan Ummi cikeda so tace “gani nan nazo, Gwaggon ki na nan dake Ummi zakiji sauki kinji, me kikeso ciki gayamini nizan miki dakaina” tai maganan tanakai kunnenta saitin bakin Ummi, ahankali Ummi tace “Gassashen dankalin hausa amurza kulikuli akai” dasauri Gwaggo tadago takalli su Shatu daduk ke tsaye tace “buhun tsaraban damukazo dashi nasa dankalin hausa? Kaina yayi chaji na manta nasaka Shatu”? Whispering Alhaji Musa yama Nura akunne yace “kai kaga zabgegen buhun tsarabane saida nabiya extra luggage fee a airport” dasauri Zakiyya tace “eh akwai” dasauri Gwaggo ta zame lullubin dake kanta taci dammara dashi aciki takalli Alhaji Musa tace “Zakiyya ta bika kabude buhun, ke Shatu samomin manyan duwatsu da makamashi na gasa mata dan kali” takalli Hadiza tace “zan sami mai” Nura dafe kanshi yayi Hadiza ma tsoron rigiman tsohuwan yahanata magana Alhaji Musa ne cikin dabata yace “Gwaggo nan asibiti ne” “yo masallaci ne dabazan iya hada makamashi ba naga ba girki zanyi ba gasa dankali zanyi” gefen Gwaggo Nura yabi yazo gaban gadon yakalli Ummi kaman yar babyn shi yace “dankali zakici gashashe?” Gyadamai kai tayi Gwaggo tace “da murjajjen kulkuli da man gyada” kallon Gwaggo yayi yace “Gwaggo saidai aje gida ayi baza’a bari ayi anan ba” dasauri tace “kaga nabar dakin nan jikata tabar shi ne su Shatu dai akaisu gidan suyi” dasauri Alhaji Musa yace “kuzo duk muje gidan sai Gwaggon tazauna” cikin turenci Nura yace “someone needs to stay what if Doctors needs anything” ahankali Hadiza tace “kaje kai inyaso saikai wanka i will stay with them” Gyadamata Kai yayi ahankali yace “thank you” shima murmushi Alhaji Musa yayı ganin changes from Hadiza, sake dukawa yayi ya shafa fuskan Ummi yace “bari muje gida okay” Gyadamai kai tayi takalli kannanta da ido hakan yasa Nura yace “Shatu kuzo” Kaman jira suke dasauri sukazo gaban gadon rungume Ummi sukayi duka sai kuka Gwaggo tace “mehaka kuka nace kuzo kuyi?” Wannan karan kowa na dakin saida yayi dariya har Nura saida ya murmusa wacce tagama kukanta yanzun nan ne take Hana wasu tashi sukayi duk suka tafi Alhaji Musa yatukasu har zuwa gidansu dasukakai gidan baki suka büfe suna kallo har flat na Ummi yakaisu gateman ya shigo da tsaraban shidai yabasu grill nashi da charcoal aciki a bayan gida shida Alhaji Musa suka fito da kayanshi da Hadiza takawomai asibiti flat nata yawuce yabude kanshi ko ina tsaf tsaf yatafi sama kaman ba gidan Hadiza ba wanka yayi ya shirya ya sauko shida Alhaji Musa sukaci abincin dake nan dinning a warmer yaşandı ba laifi sannan yatafi duba su Shatu abubku da charcoal harya gama gasawa Shatu ta daka kuli tasa maggi da dan yaji Nura yabasu kul da kanshi suka zuba yakawo musu abinci daga side din Hadiza da drinks tass sukacinye sannan yadaukesu Alhaji Musa yawuce dasu asibiti shikuma yadauki wani mota dan zuwa dauko Hajiya da Meena a airport. 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 4️⃣1️⃣ Kina neman class na matan aure da akeyi da turenci??? To look no more ga MAJAL WELLNESS nakawo muku💃 Indai class ne da ake tafarfasa karatu kan harkan abenga da turenci trust me bazaki taba samin a class better than SAMOHHACK by Majal ba so hurry and join her waitlist group ko kiyi chatting nata up now now now!!! Check out her IG page @majalwellness💃 You will come thank me later oo💃 https://chat.whatsapp.com/H50w7C7Lrbv8ZiPKzKxm5l Yana daukan su suka wuce asibitin Alhaji Musa yatafi daga Gwaggo dake bama Ummi dankalin tanaci ahankali sai Hadiza data rike mata bottle water a hannu Nura da Hajiya suka shigo dan faduwa gaban Hadiza yayi ahankali tamike tsaye tace “sannu da zuwa Hajiya” ga mamaki ta kaman bata taba samun matsala da Hajiya ba Hajiya tace “sannu Hadiza, sannu da kokari kinji Allah miki albarka” takalli Gwaggo cikeda Fara’s tace “maraba lale Gwaggo” Gwaggo itama cikin fara’a tace “Barka da zuwa Hajiya” Hajiya tabi Ummi da kallon tsantsan so da tausayi tace “ya diyata da jikinta”? Gwaggo tace “lpy lau” Kan Ummi Hajiya ta shafa saita shiga tofa mata addu’a da babu wanda keji sai bakinta dake motsi Nura ya jingina da bango kawai yana kallonsu, gamamakin Hadiza karasowa Meena tayi kusada ita kaman basu taba samin misunderstanding ba tace “ina yini Anty Hadiza” mamakin da Hadiza taji saida ya bayyana a idanunta, Meena tace “thanks for everything Yaya told us yanda kiketa dawainiya dasu mungode” murmushi Hadiza tayi tace “bakomi ai an zama daya” Gyadamata Kai Meena tayi saita wuce wajen kannen Ummi data saba dasu kusan wuni sukayi sai around 3 Hadiza takoma gida sabida su Aman dazasu dawo dağa school tareda Hajiya da Meena da kannin Ummi akabar Nura da Hajiya, sai hira sukeyi itada Hajiya tun bata sakin jiki harta saki jiki abinta a flat din Ummi suka sauka itakuma Hadiza tawuce nata tasan dama da wuya su sauka anata dudda taso hakan but bakomi with time komi zai daidaita. Sai around 11 Gwaggo takado Nura da karfi da yaji yabar asibitin badan yasoba flat din Ummi yawuce duk idanunsu Hajiya biyu basuyi bacci ba yadan zauna yana hira dasu Hajiya tace “tashi kaje ka kwanta kahuta Nura” baiyi musu ba yawuce bayan yamusu sallama yafita yawuce flat din Hadiza falon a gyare tsaf, Hadizan yagani zaune afalon ga laptop dinta tasaka reading glasses sai yau take duba harkan shagonta tana ganinshi ta ijiye laptop din ta mike saikuma ta tsaya tace “sannu da zuwa” dan murmushi yamata ya maida kofan yarufe yatako anatse zuwa inda take ahankali yace “lemme hug my wife da warin asibiti” sai kawai ya rungumeta murmushi tamai tace “my husband smells good” yadanyi one minutes ahaka sannan yasaketa zai wuce sama da sauri tace “akwai dinner zakaci ko zakasha tea”? Ahankali yace “make tea for me cus it’s late ki kawomin dakina bari na watsa ruwa” sama yawuce direct dakinshi dan kowani flat yanada dakinshi yafada bayi wanka yayi damuwa yamai yawa daurewa kawai yake fitowa yayi daure da towel yaga Hadiza takawo tea pajamas yasaka ya feffesa turare sannan yataho gently yazauna kusada ita yadauki mug na tea din yace “thank you Didi” murmushi tamai tana kallonshi yanashan tea ahankali harya gama tashi tayi tace “bari nakai kitchen” shima tashi yayi yace “bari naduba yarana” tare suka fito dakin Aman yafara shiga dake bacci ya duddubashi yamai addu’a sannan yawuce na Amali itama yamata addu’a yafito saiya bude dakin Hadiza ganinta yayi ta kwanta agado ahankali yace “taso muje mu kwanta” batai musu ba tasowa tayi tana tafiya yana binta da kallo har saida tazo dab da shi hannunta yakama yatayata kashe wutan dakin sannan suka wuce dakinshi kashe wuta yayi ita tafara shiga cikin gadon shima yahayo ya kwanta tareda jawota jikinshi faduwa gabanta yayi tanaso tayi gyara kafin wani abu ya shiga tsakanin su she prays bazai mata komiba. Ijiyan zuciya yasauke ahankali kafin yakai hannunshi yasa a tsakiyan nata suka hade murya Chan kasa yace “my Didi” ahankali itama tace “my Nuri, menene? Meke damunka? Menene matsalan Mijina? Talk to me”? Dan ijiyan zuciya yasauke yasake shigewa cikin jikinta da kyau kaman bazaice komiba chan yace “I haven’t told anyone but inaso nakai Ummi either Egypt ko India duk Wanda yarıga fitowa what do you think?” Ahankali tace “yes nima zanso hakan sabida a dubata da kyau and manage her harta haihu” Ijiyan zuciya yasauke yace “zaki dagamin kafa?” Dasauri tace “of course Nuri” murmushi yayi yace “I love you my stubborn wife” dan murmushi tayi tace “ai ka horani bazan karaba” saitai dan shiru kafin chan tace “Nuri” ahankali shima yace “Didi”. Labarin Zeenah tabashi tundaga kan case na kotu har karshe tace “Nuri I’ve been a fool, is just like abinda Anty Jams tace I am just a fool wawiya mara wayau all abinda na iya is ihu da zagi Zeenah ta cutardani Nuri she made me believe in feminism kaman an juyamin brain na zauna kan abin kaman nina kawo feminizm duniya amman nida feminizm har abada Nuri I sincerely apologize for all the pains I’ve caused you can u find a place in your heart to forgive me?” Ahankali yakai hannunshi saman fuskanta dudda baiji karan kuka a yasan hawaye yazubo dağa idanunta ahankali yace “komi daya faru between us is destiny, haka Allah ya kaddara, duk Wanda zaiyi kuskure yagane ya gyara mutum ne, babu wanda yafi karfin jarabawan ubangiji nayafe miki itakuma Zeenah Allah zaiyi maganinta ki barta da halinta delete her number bansonki da any kawa again, and your business kicigaba but anything 3 daga yanzu nakeso ki dinga dawowa gida, and weekends that’s Saturday and Sundays is for me nawane banso kina zuwa shago ranan kinji you can hire more staff to handle your work, and yarana give them your time and affection I wants Aman and Amali su soki sama da yanda suke sona make up for your mistake ki gyara tsakaninki dasu kija yaranki ajiki kinji Hadiza” gyadamai kai tayi ahankali, tace “thank you Nuri you are the best husband” ahankali yace “u are the best wife” hamma yayi, ahaka yana manne da ita bacci yayi awon gaba dashi. Almost 1months Ummi tayi anan asibitin aka gama processing komi cikin kannin Nura Ya Aisha ne kawai bata zoba itama sabida Egypt za’a kawo Ummin nan but duka kannen Nura sunzo nan da nan aka saman ma Ummi da Gwaggo komi suka wuce Egypt itakuma Hajiya tawuce kano da kannin Ummi da Meena Nura yarığa ya barmata kudi yanaso takai yaran boarding school mai kyau yama gayama Gwaggo bazai yarda ta aurar dasu yanzu ba washe garin ranan dasukaje Kano Hajiya takaisu school hadadde akai komi suka dawo gida dan amusu shopping akaisu school zasu fara JSS1 dan Gwaggo da Ummi bazasu kara dawowa Nigeria ba sai bayan Ummi ta haihu. Gidan Abuja yarage Hadiza kadai da yaranta. Dudda Nura baiso yasauka gidan kanwarshi ba but mijin Ya Aisha yace bai isaba daka shi ma yadaukosu airport Gwaggo idanunta sun kuşa faduwa akasa. Sosai Ummi tasami kulawaa asibitin da aka kaita nan ma wata daya tayi tasoma motsi da kafa da hannun ba sosai ba aka sallameta lokacin cikinta na wata biyar aka hadasu da home nurse dake managing Ummi agida 2/4/7 ga Gwaggo ga Ya Aisha shikuma Nura yabarosu yadawo Nigeria yasan Hadiza tai kokari haryau babu abinda ya shiga tsakaninsu rashin lafiya Ummi kaman ya ciremai sha’awa gabaki daya ajiki abinshi ma bai aiki yanzu dayaga tadan Soma miydi da kafa har an sallamesu yasa hankalinshi yadan kwanta. 7:30 na bayan magrib jirginsu yasauka a Nigeria Hadiza da kanta da yaran sukazo daukoshi dan yaranshi sunyi missing Babansu basu tabayin one whole month basu ganshi ba, itama Hadiza takosa taga mijinta dan tasha gyara bana wasaba har vagina rejuvenating aka mata duk suna tsaye a arrival Aman yafara hargo Babanshi da cabin size LV trolley nashi hadadde wani ihu yaron yayi yace “Daddyyyy” dasauri Nura ya kallo wajen dan ana duba bag nashi ne Amali ta fanfale da güdü tana dady Dady tai wajen Hadiza na kwala mata kira ina batasan wannan ba Aman shima ya bita wani tsalle Amali tayi. “Oyoyooo Dady” Nura yadauketa yana murmushi sosai yace “oyoyooo my princess, Amannnnn” yafadi daidai Aman na zuwa shima yadaga shi duk suka rungume Baban su saikuma sukahau kuka airport authority yace “to baga Dady yadawo ba menene kuma na kuka” ashagwabe Amali tace “I’ve missed my Dady a lot” kiss Nura yashiga manna mata a kumatu daidai an gamamai komi yafito yasauke Aman yaja jakan da hannu yaran na murna Hadiza sai murmushi take akwai wani joy da fulfillment da mata keji idan mijinta nason yaranta cus bakowani maza ke nunama yaranshi so kaman Nura ba, dan tsayawa Nura yayi nesa da Hadizan yabude hannunshi daya yace “baza’amin oyoyo ba” dasauri Hadiza ta taho akunyace ta rungume Nura Aman yayı tsalle yace “Mommy I’m right here carry me let’s hug Dady together” sakın Nura tayi tana murmushi tadauki Aman suka rungumeshi duka yanda kasan yayı shekara baya tareda su (Omoh maza is good to be a good Man oo duk randa kai tafiya aji kaman kayi shekara dari). Sakinsu sukayi suka wuce Amali na jikinshi har lokacin har zuwa wajen motan Hadiza, boot yabude yasa bag nashi yabude baya yasa yaran Hadiza ta zata mazaunin wanda ba driba ba ta kalleshi cikeda so tace “I will be your driver just for today” cikeda tsokana yana murmushi yace “thank you direba” dariya Hadiza tayi tace “Allah ko you will pay fine” ta maida kofan tarufe tazaga ta zauna mazaunin direba taja motan sai hira yaran kema babansu suna tambayan ya jikin Anty Ummi, kusan duka hiran abinda yafaru da baya nan saida sukamai amotan nan shima yabiye musu har Sauda sukakai gida. Nan ma har dakinshi suka bishi zaiyi wanka Hadiza zata hanasu yace “tabarsu shima yayi kewan yaranshi” zama sukai akan gadon shi suna jiranshi yawuce bayi dan wanka itakuma Hadiza ta tsaya a dinning tana kara gyara abinciccikan datamai daban daban saukowa sukai shiga yaran abincin ma anan kasan carpet na falo yazauna yaci barbecue chicken da Hadiza tamai ga lasagna, ga Chinese rice da salad ga fresh juice abincin duka sunyi dadi yaci sosai hakama yaranshi dan duk sunkicin abinci wai sai Dady yazo sannan yasa Hadiza tabude jakanshi takawo tsarabansu toys masu kyau yasayo musu yabasu da wasu cute kids slippers da ribbon for Amali Hadiza kuma yabata wani gold bangle mai shegen kyau sai murmushi take yaran suna murna nan fa suka dingama Dadyn su hira Amali anan jikinshi tai bacci Aman kuma anan kan carpet gefen Baban Hadiza tace “finally! Some peace” dan murmushi Nura yayi yace “zoki dauki Amali” zuwa tayi tadauki Amali shikuma yadauki Aman duk suka wuce sama suka kwantar dasu yasauko kasa ya kulle kofa ya kashe tv ya kashe wuta yawuce sama ahankali, dakin Hadiza yawuce but bata ciki tana bayi wanka take ahankali ya maida kofan yafito yawuce dakinshi ya zauna tareda daukan wayanshi dake gaban mirror dan kiran Ummi saiyaga text message nata tace “ka sauka lpy Baban Amalily? Yasu Aman da Amali? Ya kasamı Maman su? Please ka gaishemin dasu, Baban Amali inaso kahuta ka kula da kanki the past 2months kawahala da dawainiyata kaje nan kaje chan duk sabida ni, Allah yabiyaka da Aljanna nagode dakomi My Noor, inamaka so na hakika! Inason ka amiji har aljannatul Firdaus” murmushi yayi saiyay dialing number ta yaji akashe yasan da gangan takashe, Aisha yakira tana dauka tace “Yaya kasauka lpy” ahankali yace “Lpy lau kaima Ummi wayan” dasauri tace “to” kusan 1min tace “gata” tabama Ummi wayan tafice kai tsaye yace “wa yace ki kashe waya?” Kasa magana tayi yace “kinason nahadaki da Gwaggo bakisan nakira naji wayanki akashe hankalina zai tashi ba”? Ahankali tace “kayakuri” dasauri yace “noo bazan hakura ba saina hukuntaki nadawo” dan murmushi tayi murya ciki ciki tace “ka manta kan lokacin””bazan manta ba zansa a reminder” yafadi dasauri ta zaro idanu dan bata dauka yajiba yace “ya hannun da kafan”? Ahankali tace “hannuna na komi yau kawai kafan ne shima Alhamdulillah” ahankali yace “Babyna fa” dan cikinta daya Soma girma takalla tace “gashinan uhmmm munyi kewanka yau tun safe rabon damuga Dadyn Amalily” dan murmushi yayi cikeda so yace “ki kula da kanki kome kikeso kice abaki kada ki gwada tafiya idan nurse bata taredake and again kome kikeso ki kira ki sanar dani okay” gyadamai kai tayi ahankali hawaye yazubo mata daga idanu wlh mugun kewanshi take kaman taita ihu dudda babu sauti but jikinshi yabashi kuka takeyi yasan kewanshi take cikeda lallashi yace “Ummi na” murya Chan kasa tace “uhn” ahankali yace “stop crying dudda ina nan but am still there with you, zan dawo soon kaman gobe ne kinji, kidena kuka kar babyn mu yafara kuka, goge fuskanki” hannu tasa ta goge fuskanta yace “good girl ina Gwaggo bata wayan” Gwaggo dake chan falo zata kashe mijin Ya Aisha da dariya dan yanda kukasan ita ta haifeshi ta kealama kira tazo ta gaisa da Nura tace “wai yaushe ka bata Ummi haka kaga kukan datamini yau bayan katafi kuwa saida zuciya ta debeni nacema sani nima yakaini ma shiga jirgi natafi tunda ni ba mutum bane gani amman tanama miji kuka danya tafi nan fa aka dinga rokana nahakura” dan dariya Nura yayi yace “Gwaggo nidai kidena ma matana fada banso” dasauri Gwaggo tace “kaci mai garinku Nura ungo wayanki nafasa magana tunda shakiyanci yake mini” sallama yayi da Ummi sannan ya ijiye wayan yatashi yafito dakin Hadiza yatafi hartazo taji yana waya hakan yasa takoma dakinta batason takatse shi kuma bataso taji abinda zaisa kishinta yatashi. Tana zaune gaban mirror tana shafa lips sleeping mask na lineage yashigo wasu crazy kayan bacci ne ajikinta ga fararen cinyoyinta awaje dakin yana wani lafiyayyen kamshi binta yayi da kallo kafin ya tsaya daga wajen yace “yammata jimana” juyowa Hadiza tayi tamai wani kallo kashe mata ido daya yayi yace “zomuje zaure minti daya” dan jaye riganta sama tayi tawani shafa cinyoyinta tace “matsema Maman mu ni zakayi?” Dan waige waige yayi kaman irin akwai mutane wajen, cikin whispering yace “makota zasuji fa” cikin iskanci Hadiza tace “Mommy somebody is trying to touch my pant” dasauri Nura yazo wajen yakama hannunta yadaga tareda tura kujeran ya matseta abango yace “is it only pant? I will also chop what’s underneath the pant” tana kallon kwayar idanunshi tace “you are so naughty Nuri” yana kallon lips nata dake shinning yace “I love naughty Hadiza nima” wani kalan ture kirjinshi tayi yayi baya baya ta cigaba da tureshi har saida sukakai wajen gado yafada gado yace “what are you trying to do I will call my Momy for you” hannunta ta daura a lips tace “if you scream Mommy I triple your punishment” cikeda iskanci Nura yace “Mommy” Dawani kalan sauri Hadiza tai kneeling tace “you asked for it, don’t beg me anjima” tawani ja wandon pajamas dinshi zutttt kasa Nura yace “jar ubanchan! Didi wani punishing za’amin”? Hanunta takai tana lamisan wajen tace “I want to suck your cock, zan sha maka zakaran dake kasan maranka harsai tayi kukkurukuuuuuuu……” 💫MATAN?? Ko MAZAN??💫 ✍🏻M SHAKUR EPISODE 4️⃣2️⃣ Tass Hadiza ta gogema Nuri hadda shi yama kasa yarda Hadiza ce haka, like is this Hadiza?? Dan he enjoyed every bit of love making dasukayi gashi ta tsuke kaman ba itaba ga dadi gashi tacishi da kyau saiyaji baida ragowan gajiya ajiki anan suka zube gado sukai bacci mai dadi. Wani kalan rayuwa take da Nura saitakega kaman yanzu ne ma take fahimtan waye Nura bala’in girmama junansu suke, bata da yar aiki most time da safe shikema yaran wanka yamusu brush ya shiryosu tsaf saidai su sauko shida yaran da ita suyi breakfast, yanzu ne take kara sonshi take gane ashe ada Nura bai rainata ba, nothing beats kina living baby girl life miji na kula dake, what is feminism? Trying to be in charge akan uban mene? Ai duk Wanda yabar koyarwan Annabi ya bace, babu abinda yakai namiji ya killace ki yana sangartaki kina karkashin sa, feminism jakanci ne da wahala da dunbin bacin rai aciki dan bazai taba barinki ki fahimci mijinki ba saisa ta salamun salama dashi har abada kuwa kawayen da meeting din ta zubar da su kaman yanda mijinta ya umurceta, Zeenah ma wasu customers dasukazo shagonta tana suna labarin mijin yamata duka ya Koreta tareda danna mata saki uku, tasan kuma alhakin ta ne, kullum cikin istigifari take, one thing is yan uwan Nura bazasu taba mata son dasukema Ummi ba amman dai yanzu bata da matsala dasu duk sun shirya, tana kiran Hajiya akai akai taji yajikinta, iyayenta ma yanzu tana kyautata musu tasayama Babanta sabon fili an fara sabon gini kal zasu koma chan gidan nan yace zai maida makaranta. Wannan kenan. ** Nura yakanje Egypt yadubo Ummi bayan kwana biyu kuma yadawo, tana 8month aka sake admitting nata a hospital wannan karan Dr yacema Nura sai ta haihu za’a sallameta. Wata rana Nura baya gari yakoma Abuja sabida wani contract dazaije yayi sealing tafara labour da CS Ummi ta iya ta haihu ta haifo two bouncing baby boys aka kira Nura haukane kawai baiyiba one week aka sake riketa asibiti sannan aka sallamota hannunta na aiki but kfafun sai a slow Nura ranan ya iso shima kaman zai cinye yaranshi kaman baturai komi na Baban su basuyi kama da Ummi koda yatsu ba. Nan aka cigaba dama Ummi physiotherapy ahaka ahaka tana koyan tafiya tazo tafara yaran na 2month suka dawo Nigeria lokacin kanninta sun dawo daga Hutu school duk aka hadu akazo suna wanda Nura yahada lafiyayyen gaske. Aranan da daddare dudda akwai mutane gidan Ummi tabi Nura dakinshi dan yashigo ita bama tasan ko dakinta zai kwanaba tana shiga dakin tafada kanshi tafashe da kuka tace “wlh duk nayi tsatsa kamin kankara Baban Amalily, ka kankareni kaji” tashi gabanshi yayi Ummi ita kadai ta iya batsanta aduniya, yana kallonta yayi murmushi ganin yanda take kukan iskanci tana kokarin kama gaban wandonshi yasa yace “Harija kawai saina dura miki wani cikin yanzu kifaramin wasiyan zaki mutu” atare duk sukai dariya kaman mahaukata daga ita har Nuran, daidai lokacin Hajiya ta kwala mata kira tace “Ummi zoki bama Husaini Nono yana kuka” kaman zatai ihu tace “nafasashi bacci” Nura yamata gwalo yace “jekizo anan zan kwana nima nagaji watanmu nawa bamu buga wawatsula ba” wanan kalan dariya tayi yanda yarike kalman tas tace “ina sonka Baban Amali” ahankali yace “nima ina sonki Maman Biyu, bari naje nama Hadiza saida safe” dasauri Ummi tace “kace mata nagode da farfesun data bani Anty is the best” “she really is!” Nura yafadi yana murmushi dan Hadiza yanzu is his pillar bata bashi matsala at all ta chanza totally, yanason duka matanshi da yaranshi and Alhamdulillah baida matsala da kowacce cikinsu yanzun ne yasami that peace daya dade yana nema. ALHAMDULILLAH!!! END!! This Chapter is about feminism, I know so many people basuso Hadiza takoma wajen Nura ba, I use the opportunity to teach us forgiveness, duk girman laifi Allah yana yafemana duk girmanshi madaman ba shirka bane! Me Hadiza tayi dazakuce she don’t deserve forgiveness bai kamata Nura ya komar da ita ba? Kunce hakan danayi zaisa masuyin feminizm su bada himma su cigaba sabida sunsan za’a yafe musu daga baya? Let’s forgive each other, mu yafema wanda da wacce tamana mistake. Maza can love you and can love another person, don’t ever believe cewa sabida mijinki na sonki sosai bazai taba iya son wata ba🥰 My dear a man can love you like mad, and can also love another woman like mad, the truth is NOTHING keeps a man saidai addu’a da hakuri. The foundation of aure is love, hakuri and respect, ku mutunta juna, ku karrama juna, ku so junanku sannan kurike Allah kukai haka aurenku will prosper. My fellow woman ha’aaaa are we not baby girls for life??? Why dragging namiji da matsayinshi na namiji please and please iyye??? Please mu zubar da feminizm din nan let’s be the babies while our men na kula damu, do your man thing I do my woman thing. I kno w I’ve made lot of mistake koma menene ina rokon Allah ya yafemini kurakuran dake cikin this book yakuma amfanar damu da abubuwa masu kyau na littafin nan, Allah ya shiryan damu gabaki daya Allah yahadamu a Aljanna! Please and Please support me in this chapter 2 by sending just 1k and subscribe nasaki a group thank you. KINDLY MAKE YOUR PAYMENT NA 1k and chat me up by clicking on this link; wa.me/+2347012181461 You can make payment 1k here 👇🏼 3107021073 Aisha Muhammad first bank KO 6353995766 M Shakur world Moniepoint Send evidence of payment I will add you to chapter 2 group. Chapter 2 is about CHEATING and I will break it down for you da yanda ake yakanta daga zuciya. TRUST ME saiyafi CHAPTER 1 dadi!!! Thank you for Reading MATAN KO MAZAN!!! Mu hadu a chapter 2 dazan fara on MONDAY💃 M SHAKUR✍🏻